Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Wednesday, May 24, 2017

MIJIN 'YAR UWA TAA

adsense here

[18/06 8:24 am] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆🍆MIJIN YAR UWA TAA 🍆🍆🍆🍆 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~1⃣~ BISMILLAHI RAHMANIN RAHIM*********** Gudu take yi kamar ranta zai, fita dandazo yara 'yan makaranta islamiyya sa'ani ta suna biye da ita sai faman kwalla mata kira sukeyi da karfi ta banki "gate tafada cikin, gida bata ankara ba taji tayi karo da mutum tana dagowa taga waye tayi karo da shi, sai kawai taji saukar marin akan fuskarta cikin bacin rai ya finciko wuyanta sai da hijab dinta ya yage yakara wanka mata mari bakinta yafashe, tsananin zafin marin ya yaratsa kwakwalwa ta ta kurma mahaukacin ihu yaran da suka biyo ta suka ja birki, bakin "gate" cikin konar zuciya yafara magana ke wace irin 'yar iska ce Raheela"? Babu ranar da za ta fadi baki daukowa mutane magana ba yau, kuma wace masifa ki ka dauko dandazo 'yan makaranta suka biyo ki"?Raheela da ke dafe da kumatu duk zafin marin da taji bai sanya ta yin, kuka ba tadago dara-dara idanuta masu kama da madara tace ni ba abun da na yi musu kawai hakki'na na kwata shine don tsabar iskanci suka biyo ni sai kace na sace kayan uban'su daya daga cikin yaran da ke tsaye, suna jiran ko ta kwana tace karya ta keyi ya Amar kudin umma naa da ta aike ni da su ta kwance harara Raheela ta galla mata hade da cewa karya ta ke yi min yaa Amar itace ta aza kudin umma'taa, tace duk wanda yasan ya cika cikkake dan iska ya je ya daki duwawu wata "copper" za ta bashi naira dari shine sai da na daki duwawun "copper" din tace ba za tabani kudi naa ni kuma na gwada mata na fi ta karfi na fisge kudin tun lokacin da tafara zu ba yake mata kallon tsana yace kaicho ki Raheela ke kan kin ji takaici kin zama fitinaniya yarinya, yanzu duk yawan yaran nan arasa dan iska sai ke ya murde mata kunne sai nacire wannan shegen kunne da baya jin magana bata kudin'ta tun kafin na banballa ki' Raheela ta turo dan karami bakinta mai dauke da "pink lips" cikin tsiwa da fitsara tace ka yi hakuri yaa Amar ba zan iya bayarda kudinan saboda hakke'na ne cikin bacin rai Amar ya rufe ta da duka sai ihu takeyi hade da cewa saidai ka kashe ni yaa Amar amma kudinan sai nasha "viju milk" da su jin kalaman'ta yakara harzuka Amar yasa hannu ya buge mata baki ta kwalla razanane ihu ta shafi bakin'ta da ke zu bar jini gani jini a tafin hannuta yasa ta takarkare iya karfin'ta tana kwadawa mami kira Amar ya yasa hannu cikin aljihu yafito da naira dari biyu sabuwa dal ya, juya wurin yarinya mai kudi yace zo ki karbe kudinki kuma duk ranar'da nakara jin kin aza kudi don wani yadaki duwawu "copper" sai na ci ubanki' yarinya ta ja tayi tsaye tana tsoron takarasa wurin Amar ya danke ta gani taki karasowa yasa ya cilla mata kudin tace yaa Amar banida canji ya galla mata harara, yadauki Raheela ya daura ta bisa kafadar'sa ya nufi dakin'shi da ita karaf idanu Raheela suka sauka bisa fuskar Na'eema tafara kwadawa Na'eema kira yaya Na'eema dan "Allah ki taimake ni yaa Amar zai kashe ni wayyo yaya Na'eema da gudu Na'eema ta bi bayan su Amar yana shiga daki Na'eema na faduwa cikin tashi hankali ta ajiye Jakarta mai dauke da lifftafai bisa "stool" Amar ya kalli Raheela da "sexy eye's" dinshi yace me ki ke jira dan gidan'ku da ba za kifara ba sai Lokacin tafara hawaye saboda tagano abunda yake nufi Na'eema ta karaso wurin shi da 'yar sanyaya muryar'ta tace dan Allah yaa Amar ka yi hankuri, ba za takara rashin ji ta juya wurin Raheela da ke tsaye tana zullumin masifar da za ta tunkara tace kindaina koh Raheela"? Cikin rawar murya Raheela tace wallahi yaa Amar nadaina ba zan kara ba... 🍆🍆🍆MIJIN YAR UWA🍆🍆 TAA🍆🍆🍆🍆 ~2⃣~ Amar ya kai mata rankwashi, aka yace kar'ma kidaina fitsarariya banza da wofi ke kenan kullum cikin tsokana da daukar magana za ki yi tsalle kwado ko sai na hada ki da "belts"? Da sauri Raheela tafara tsalle kwado Na'eema ta riko hannu yaa Amar, tayi kasa da murya,hawaye na zuba daga idanuta tace dan girman Allah yaa Amar, kayi hankuri ka kyale ta ba za ta kara ba yaa Amar ya shafi kumatu Na'eema yace shikenan Na'eema na hankura ke kadai ki ke jin tausayi wannan 'yar iska ita bata tausayi kanta ya juya wurin Raheela da ke tsalle kwado tana haki ga wani dan uban gumi da tahada yadaka mata tsawa ke mike tsaye a rude ta mike sai faman share gumi da yagage hijab dinta take yi ga kuma bakin'ta da ya kumbure yaa Amar ya nuna ta da yatsa yace duk rana da na kamaki da dukan duwawu "copper" sai na wanke miki naki da tafasashi ruwan zafi Raheela ta zaro idanu ta tsari yaa Amar da kallon tsoro cikin rawar murya Na'eema tace yaa Amar ruwan zafi fa"? Yaa Amar yace Kwarai, kuwa ruwan zafi in kuma tana gani Kamar wasa nakeyi ta sake aikata abunda ta aikata ki, ga yanda zan kona duwawuta da ruwan zafi, Na'eema ta riko hannu Raheela ta ce insha Allah ba za takara ba yaa Amar Ya tabe baki yace ina kudin mutane"? Raheela da tafara tsorata da furucin yaa Amar tace ga su nan ta nuna cikin wando uniform" dinta yaa Amar yace oya kawo su nan da sauri ta zuge zariyar wando'nta ta tura hannu cikin "pants"dinta ta ciro naira dari ta mikawa Amar zaro idanu yayi cikin kidima yace ke yanzu tsabar iskanci ki rasa inda za ki boye kudi sai cikin"pants" lallai iskanci ki ya kai a buga shi a jarida Na'eema ta kyalkyale da dariya tace kai yaya wace irin jarida kuma"? Raheela ta kara mika masa kudin, ya galla mata harara yace in ki ka kuskure kara miko mini wadanan kazaman kudin sai na karya miki hannu Na'eema da ke ta faman kyalkyale dariya ta dauki jakkar littafan'ta suka fice daga dakin, Raheela ta ja dogon tsoki hade da cewa mugu kawai baqin azzulumi wallahi sai narama abunda yayi min Na'eema ta bude idanu fuskarta dauke da mamaki tace ke Raheela ki raba kan'ki da shiga hurumin yaa Amar ba irin su yaa Abdul bane da ke Juri iya shegenki, Raheela ta fisge hannuta daga rikon da Na'eema ta yi, mata tace aka wane dalilin zai dinga jinga ta sai kace jaka ko ina ruwan'shi da ni yadda yadaura min karan tsana ni ma haka na tsane shi, wallahi na tsani in bude idanu na naga yaa Amar "Allah yasa ya mutu kowa ya huta da baqin hali shi da sauri Na'eema ta kaiwa Raheela duka tace kan'ki daya kuwa Raheela "? Miyasa za ki yiwa dan uwanki fatan mutuwa"? Don kawai yana miki fadan so kanki haba Raheela duk abunda Yaa Amar yayi miki yayi ne don yana son'ki "datz why" yake adawa da munana dabi'u ki ke ce kawai ki ke danganta hakan da kiyayya Raheela ta ja tsoki tace sau nawa yana fada min ya tsaneni ba ya sona har cewa yayi akan kiyayya da yake min zai iya yanka ni..... EXCELLENT WRITER'S Jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:24 am] Jeeddah Aliyu🌹: ￿￿￿￿🍆🍆🍆🍆🍆￿MIJIN YAR UWA TAA￿￿￿￿🍆🍆🍆🍆 Na Hauwa Shehu Aliyu￿🌹 ~￿3⃣~ Tuni nagano cewa yaya Na'eema kinfi so yaa Amar akaina, da sauri Na'eema ta riko ta tace haba "lil sis" kidaina fadar haka daga ke har yaa Amar nawa ne kuma ina goyon bayan'ki da ki rama abunda ya yi miki Raheela ta, yi murmushin jin dadi ta rungume Na'eema tace ina son'ki yaya Na'eema taa Na'eema ta janye ta daga jikinta tace wuce mu tafi gida kar kije ki kara dauko muna wata sabuwar rigima don ke kan daukar magana ba wuya yake miki ba, Raheela ta turo baki ciki shagwaba tace kai yaya Na'eema wace rigima nake daukowa? Duk lokacin da ki ka anyi rigima da ni to tsokana'ta akayi kin kuma san ni ba kyalewa zan yi ba Na'eema ta girgiza kai tasaka Raheela gaba suka shige cikin gida suna kada kafarsu tsakiyar gida Raheela ta daka tsalle tayi faduwar 'yan bori ta dagargaje iya karfin'ta tafara kurma ihu sai kace wanda uwa da ubanta suka mutu a hatsari jirgi sama, Na'eema ta koma gefe tana kallon iko "Allah saboda tasan wannan yana daya daga cikin hali Raheela a zuciyata tace yanzu nan 'yan kori ta guda biyu za su fito kowane da yanayi tashin hankalinsa dattijuwa 'Yar kimani shekaru tamani ta fito daga dakin'ta zani ta a hannu ta nufi wurin Raheela da ke ta faman zunduma ihu hade da shure-shure ta riko hannaye ta a rude tace babur ne ya buge ki Raheela? shine don tsabar mugunta irin ta 'yan achaba yakasa kai ki asibiti yasauko min ke jina-jina to Allah ya esa baki yafe ba, Na'eema ta yi murmushi sakamako gani yaa nazeer ya shigo a firgice da sauri yadago Raheela yace wai me ke faruwa ne kaaka tun daga "side" din mamee nake ji ihu tawan"? kaaka, ta gyara dauri zani ta, tace dan achaba ne ya buge ta kuma don.....Na'eema ta katsita ta hanyar cewa ba fa dan achaba ne ya buge ta ba, kaaka ta galla mata harara tace to uban waye yakeda jarumta daka mini yarinya haka"? cikin sanyi murya Na'eema tace laifi ta yi yaa Amar ya hukunta ta, a harzuke kaaka ta tasowa Na'eema kamar za ta cinye ta danya tsantsan masifa da bala'e suka baiyana akan fuskarta, bakinta Sai faman kumfa yakeyi sai kace wanda tasha omo" wai Amar wane irin mugu ne da baya kaunar a zauna lafiya"? sau nawa ina yi masa gargadi yadaina daurawa raheela hannu da yake shi, dan banza ne sai yayi kunne uwar shegu da magana ta amma ba komai yau zan ga uban da ya tsaya masa a gidanan, yaa nazeer ya ja tsoki yace wallahi kaaka in baki dauki kwakwara matakin akan irin dukan da yaa Amar yake yiwa tawan wata rana gawar'ta za'a kawo miki a gidanan kaaka ta zaro masifafu idanu'ta tace cabdijam gawa fa kace nazeeru ashe kuwa Za'ayi yakin basasa na biyu a gidanan, tashi mu tafi wurin uwar'sa taga abunda yayi miki ta fisgo hannuta suka nufi "side" din mamee yaa nazeer ya mara musu baya Raheela sai faman gunji kuka take Na'eema da ke tsaye tana kallon "drama" ta tabe baki a baiyana tace Raheela sarkin rigima yanzu kuma ta janyowa mamee masifa da bala'en kaaka tun daga "gate" din gidan kana jin sautin muryar kaaka tana zuba ruwan rashin mutunci a firgice mamee tafito daga kitchen" hannuta rike da ludayin miya tace kaaka lafiya wannan fitinaniya ta ke yiwa mutane karadi a gida sai kace wanda aka kwakwalewa idanu"? Jin furucin mamee yakara harzuka kaaka tace dan'ki ne fitinanne kuma wannan zuwa da nayi kashedi na karshe na zo nayi miki ,ki jawa Amar kunne yafita harka Raheela babu ruwan shi da ita ya kauda idanu shi, a kanta ko na dauki mumuna mataki akan'shi don tsabar mugunta zai zage dantse ya dinga narka yarinya sai kace baiwa ubanshi to wallahi ki jan masa kunne matukar yanaso zaman lafiya yafita daga sabga Raheela, tun lokacin da kaaka tafara yankar kauna mamee take kallon'ta inda sabo tasaba da cin mutuncin kaaka akan Raheela mamee tasauke ajiyar zuciya tace oh ni maryama naga takaina Amar ba zai daina dauko mini jangwan narasa dalilin da yasa ba zai zubawa Raheela idanu kamar yanda kowa ya zuba mata idanu a gidanan uwa da uba da suka haife ta sun zuba mata na mujiya in banda daukar magana irin na Amar ina ruwan'shi da ita kaaka takara hasala tace, dama ina sane da ku a gidanan jira nakeyi nasami sarari na wanke muku allo ku tass duk lokacin da aka azaluncin yarinyar nan nayi magana sai ku buge da yada mini gori ku ce a zuba mata idanu, kar ku zuba mata idanu ku zuba mata baki bakake munufukai, duk mugun alkaba'e ku akan 'ya'ya ku zai qare zo mu tafi Raheela "Allah yasaka miki dukan'ki da ya yi kuma ina zaune zai esko ni sai naci masa mutuncin, ta riko hannu Raheela suka fice nazeer yace gaskiya mamee ki dauki mataki akan yaa Amar yadaina exercises" akan 'yar mutane duk yawan "gyms machine" din da yake da basu esheshi motsa jini ba sai yasauke hannu shi akan 'yar mitsitsiya yarinya wannan yawa ne mamee"ki yi masa "warning" yadaina shiga gonar kaakus saboda batada kyawo, mamee ta nuna shi da ludayin da ke hannu'ta tace Ka kiyayye ni nazeer duk wannan iskanci da bankada da Raheela ta ke yi ae kai da kaaka ke Kara zugata baku San wannan son da ku Ke nuna mata, cutar ta ku ke yi ba sai ranar da ta janyo muku masifa da za ta kai ku gaban alkali, daga Lokacin za ku fara karatun ta natsu, maza ka fice min daga falon tun kafin na huce haushi kaaka akan'ka nazeer ya juya yana gunguni kaaka na rike da hannu Raheela suka nufi "Side" dinta yaa Amar da ke tsaye a "parking space yana kallon taya motar'shi da aka suce iskan tayar' ya tsinkaye kaaka da Raheela yasan qara shi, aka kai wurin mamee yayi sauri ya boye bayan mota sai da kaaka ta wuce sannan yafito, ya kalli taya motar shi wani irin bacin rai ne ya lullube shi yasan wannan aikin Raheela ne kenan dukan'ta da yayi da safe shine ta rama ga taya motar'sa.... 🍆🍆🍆MIJIN YAR UWA🍆🍆 TAA🍆🍆🍆🍆 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~4⃣~ Kaitsaye ya nufi bangare su yana shiga falon ya ci karo da mamee zaune harara tafara aika masa daga bisani tace burinka yacika Amar kaaka tashigo, ta wanke mini allo'na tasss Amar yanemi daya daga cikin kujeri falon da ke "facing" din mamee ya zauna mamee tacigaba, da yi mishi fada na roke ka Amar kadaina shiga sabgar Raheela inda abunda takeyi yana damunka, to kayi mata addu'a Allah yashirye ta kadaina dukan'ta ita kuma nata yaranci ne ya zo da haka da takara girma za ta tadaina, yaa Amar yatsine fuska daga bisani yace Wane irin yaranci mamee?" yarinya da take da 13 year's itace kullum za ku dinga danganta ta da yarinta wannan iskanci da take shekawa yayi yawa duk wanda yake unguwar nan yasan'ta kuma yanada labarin kwaranniyar'ta, mamee tasauke ajiyar zuciya tace wasu lokuta bana gani laifin raheela saboda kaaka ce ta jagoranci tabarbarewar tarbiyar'ta kawai abinda nakeso da kai kadaina dukan'ta, yaa Amar ya mike tsaye, yace mamee aro min "key's din daya daga cikin motocin "daddy" mamee ta bata fuska tace kai ina taka mota ne"? Ya dan Sosa kai yace,tayi facin kuma banida lokacin, jiran labaran ya chanza taya saboda sauri nakeyi, mamee ta tabe baki ta mike tashiga "bedroom" din daddy ta dauko masa keys din ta bashi yafice daga gidan, kaaka da Raheela na shiga falon" kaaka tacigaba da zazzaga masifa da bala'e Na'eema da ke kwance bisa "three star" ta juya wurin kaaka tace haba kaaka dan "Allah ki barmu mu huta tun dazu ki ke abun daya matukar aka kyale ki za ki iya kaiwa gobe kina wannan fadan na rashin dalilin, kaaka ta watsa mata harara tace ke Na'eema banaso munafunci ina ruwan'ki da fada na naga nan falon'na ne in har kinji baki iya juri fada na sai ki, tattara komaitsa ki" ki koma bangare ku. Na'eema tayi murmushi hade da cewa Allah yabaki na mai bara kaaka. Cikin zafin rai kaaka tace "ameeen..... 🖊EXCELLENT WRITER'S Jeeddah Aliyu🌹 [18/06 8:29 am] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆🍆MIJIN YAR UWA TAA🍆🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~7⃣~ Tsananin son da Abdullah yake nunawa Amar yakara saka hajara cikin, kuncin da baqin ciki, don haka tabi ayarin 'yan uwata na kaiwa bokaye da 'yan tsinbo kudin'ta don, taraba Abdullah da 'yan uwan'shi saidai kash aikin bokanta baiyi tasiri akan Abdullah ba gani haka yasa ta koma neman haihuwa idon rufe, taje asibiti likita ya tabbatar mata da cewa lafiyar'ta qalau lokacin ne, na haihuwa'rta baiyi ba amma hajara kasa hankura tayi tasoma amfani da maganin da bokanta yabata wai za ta haihu haka ta dinga daurawa cikin'ta najasa. Saida Amar Ya shekara hudu a duniya fateema takara haihuwa da namiji aka rada masa suna nazeer. Hajja rahee nagani hajara tayi shekara bakwai ko 'bata wata bata taba yi ba tayarda masifa da bala'e sai abdullah yakara aure ana cikin wannan rungutsumi, sadeeya kanawar fateema ta kamalla karatun ta na sakadire ta zo gidan fateema hutu tun da Abdullah ya kyala ido yaga sadeeya yace yaga Matar aure tun fateema nadaukar abin da wasa har tagano cewa Abdullah da gaske yakeyi, daki tasaka sadeeya ta ja mata kunne tafita da harka Abdullah saboda baza taba amincewa Abdullah aure ta don tasan kishi da hajara masifa ne ga sadeeya shiru-shiru ce sai ka yini da ita bakaji tayi magana ba, wasu har tsanmani sukeyi ko kurma ce, duk jan kunne da fateema tayiwa sadeeya bai shige ta ba domin kuwa soyayya sukeyi kamar su cinye junan'su, lokacin da Abdullah ya gabatarda sadeeya a wurin hajja Rahee ba karamin farin ciki tayi ba tace ae gara auren 'ya'ya buzaye da zama da juya da yakeyi, batare da sani fateema ba Muhammad yanemawa Abdullah aure fateema, Lokacin da fateema taji labarin har kuka saida tayi saboda tasan hajara sai ta zargi cewa ita ta hada auren abdullah da kanwar'ta sadeeya. Hajara batasan Abdullah zai kara aure ba sai ranar'da za'a daura aure, wannan duk "plain din hajja Rahee ne a cewa ba za'a sanar'da hajara da wuri saboda kartaje wajen bokaye ta, ta wargaza auren rana da aka daura aure ranar amarya ta tare lokacin da hajara taji abdullah zai kara aure sai tayi 'yar karamar hauka nan take 'yan uwan'ta suka cika gida sai faman zugata sukeyi, wata yayar'ta mai suna asabe ta gyara zaman mullamulai duwawuta bisa kujera tace kaico ki hajara kin janyo muna abin fade a garin Kin barwa zuri'ar sambo da lami tarihi domin kece ta farko ta kuma karshe da aka fara yiwa kishiya, don tsabar iskanci da dakikanci irin naki, sai ki ka mike kafafu batare da kin datse kofar gidan'ki da katon "padlock ba to gashi nan irin wauta da saken da ki kayi ya janyo miki zama inuwa daya da bakar kadara kuma wani abin haushi wai ko sunan amaryar, baki sani ba. Hajara tasauke katuwar ajiyar zuciya tace wallahi Anty asabe duk wata nake kaiwa lami kudi tana karbo mini taimako wurin malam mai allon karfe, kuma bana wasa da kayan mata" asabe taja tsoki cikin zafin rai tace tun 1986 aikin malam mai allon karfe yadaina ci, duk aljannu shi yanzu na karya ne, ke in zaki falka daga baccin ki falka ki zo aikai ki wurin boka bakamu mai gani har hanji shine, kadai yake da maganin matsalarki, cikin tsananin farin ciki hajara ta amince da hudubar shedan din da 'yan uwata sukayi mata. tsabar zafin kishi irin na hajara yasa takasa fitowa lokacin da aka kawo, amarya balle taga fuskar kishiyar'ta sai a washe gari da Abdullah yakira su don yayi musu nasiha, su zauna lafiya hajara na shigowa taci karo da fuskar sadeeya zaune kusa da mijin'ta, cikin sarkewa murya tace Abdullah badai sadeeya kanwar fateema facalla ta ita ce amaryar'ka"? Abdullah yayi murmushi, yace ita ce mana ae nasan za ku zauna lafiya saboda sadeeya ba ruwanta akwai hankali da natsuwa...... 🍆🍆🍆MIJIN YAR UWA🍆🍆 TAA🍆🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~8⃣~ Hajara ta zaro idanu ta masu kama da idanu 'yan China" tafisgo dan kwali'n kanta tasha damara tace kan uban nan lallai kuwa Abdullah ka cika cikkake mayaudari Maciyi amana, yanzu duk 'yan mata da ke cikin garin kaduna karasa wanda zaka aura sai sadeeya"? Babu abinda yau zai hanani naci ubanki siddiqu dan agadaz a gidanan tayi kukan kura ta afkawa sadeeya da duka da kyar Abdullah ya kwance sadeeya hannuta sadeeya sai faman kuka takeyi, saboda batasaba da halin karnuka ba abdullah ya riko hannuta yakaita "side din fateema duk da haka nan saida Hajara tabin su tasaukewa fateema kwadon tijara Hafsat ta sheka da gudu side din hajja Rahee tace kaaka ana fada da mamee da umma Anty sadeeya sai faman kuka takeyi nan take hajja rahee tagano abunda ke wakana, mikewa tayi ta nufi "side din fateema tafada cikin falon dai-dai lokacin da hajara take cewa, kudai yi abun kunya ya da kanwa suna aure gida daya don tsabage kwadayin a mallake abin duniya dama ci rani aka zo matukar ina raye bazan zauna da sadeeya a matsayin kishiya ba. Ke dakata 'yar gadon mugun abu to aniyar ki ta sharri tabi ki hajja Rahee ce ta daka mata tsawa, hajja tacigaba da cewa da ba'a aure ke da ana auro ki, mafi alkhairi a tare da ke ki zauna lafiya da sadeeya ko kuma kiyi waje road" don ba ki zo da "block's a gara ki ba ballatana ki nuna mana baqin mulki da lami take yiwa sambo kiyi maza ki bace mini da gani 'yar gadon rashin tarbiya da sauri hajara tafice, daga falon saboda duk iskanci'ta tana masifar tsoron hajja. Hajja ta juya wurin Abdullah tace kai kuma tun da kace za ka iya to kuwa dole ka jajirce ka zama tsayaye namiji in ba haka ba, hajara za ta mayar'da kai shanyaye kamar yadda uwar'ta ta mayar'da ubanta, tana karasa zanceta tafice daga falon fateema da Abdullah suka cigaba da rarrashin sadeeya tun daga ranar da sadeeya tashiga gidan,abdullah a matsayin matar'shi tayi ban kwana da farin ciki da kwanciyar hankali saboda hajara ta tsare gaba ta tsare baya duk don gani ta fitar'da sadeeya daga gidan Abdullah kowa ina taji labarin sabon boka sai ta kai mishi ziyara saidai babu biyan bukata kwatsan ana cikin wannan rungutsumi sadeeya tasami ciki saura kiris hajara ta hadiye zuciya ta mutu abunda take nema shekara da shekaru bata samu ba sai gashi da shigowar sadeeya tasamu tun daga, lokacin tasha al'washi sai ta zubar'da cikin duk wurin boka da taje sai yace mata tabbas sai sadeeya ta haifi cikin nan abinda yakara daga mata hankali kenan bayan wata tara sadeeya ta haihu tasami "twins" duka maza rana da ana mutuwa adawo da sai hajara ta mutu tadawo, don tsabar bakin ciki kasa zuwa tayi taga yaran ranar suna ta zagayo, aka radawa yaran suna abdulhakeem da abdulhaleem haka rayuwa tacigaba gaba da tafiya, wasu na cikin jin dadi wasu na cikin wahala sadeeya, tana daya daga cikin mutane da ke cikin wahala, saboda batada 'yanci tafito tsakiyar gida yanzu hajara na fitowa tafara zagin'ta ta, uwa ta uba ga sadeeya ba iya ramawa takeyi ba "twins" na da shekara uku sadeeya takara haihuwa wannan karo ma "twins ta haifa kuma duk maza aka rada musu suna sadeeq da saleem. Ranar hajara daki tashiga ta rufe kofa tadinga rusar kukan baqin ciki tana cikin wannan halin kwatsan Anty asabe ta kawo mata, ziyara gani halin da hajara take ciki yasa ta tausaya mata ko zama batayi ba, tace tashi mu tafi daga wannan lokacin kinyi ban kwana da baqin ciki... 🖊excellent writers🖊 Jeeddah Aliyu🌹 [18/06 8:29 am] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆🍆MIJIN YAR UWA TAA🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~9⃣~ Hajara ta share hawaye fuskarta ta dauki mayafi da jikka suka fice daga, gidan drivern Anty asabe sai faman sharara gudu yakeyi kamar wanda zai bar duniya tuni sun fita daga cikin garin kaduna yana dauki hanyar Niger state" saida yayi kusan shiga garin minna sai kuma ya yanke wata hanya wanda babu kwata akanta sai jar kasa, haka ratsa daji daga karshe yasami wata 'yar karamar rugga fulani yayi, parking" saboda babu hanyar da mota za tabi zuwa gidan bokan suka fito daga cikin Mota suka soma tafiya da kafa, driven yana gaba suna biye da shi saida sukayi tafiya mai nisa gaske tun nesa suka hangi gidan boka duguzuu zana ce kewaye da gidan sai kayan tsafi da ke daure jikin zanar bukoki ne guda biyu a cikin gidan,Komai girman jikin mutum ba zai iya shiga cikin bukar ta tsaye dole, sai ka duqa saboda kankata kofar babban tashin hankali na farko da za ka fara fuskanta daga jefar kafar ka tsakiyar gidan boka duguzuu, shine wari ,wani masifafe wari na fitar hankali gidan yakeyi hajara ta toshe hanci ta da sauri anty asabe ta buge hannu'ta tace kinga hajara ki rufawa kan'ki asiri ki kuma rufa mini ni da nayi sanadiyar zuwan ki gidanan, karki kuskure ki qara toshe hancin'ki saboda abinda boka duguzuu yatsana kenan in kuma ki ka bari yaganki zai mayar'da ke abar kwatance hajara tafara tsorata da jin furucin Anty asabe. Drivern anty asabe yace hajiya ni zan tsaya daga nan sai ku karasa cikin,bukar Anty asabe ta wuce gaba hajara ta mara mata baya suna karasawa bakin kofar suka ji wani irin masifafe wari yana musu barka da zuwa Anty asabe tace "ahuuwanku" gafara dai boka duguzuu dan hasarariya wata mushirika dariya suka fara ji tana fitowa daga cikin bukar gaba daya dajin yasoma amsa amon dariyar tasa, tsawon lokacin yadauka yana kwasan dariya daga bisani yace barka ku da zuwa 'ya'ya hasarari barka ku da zuwa abokan zuwa jahanama, barka ku da zuwa fadar boka duguzuu dan asarariya ku shi ku da kafar hagu a lokacin daya fargaba hade da firgicin suka ziyarce hajara jikin'ta yafara rawa Anty asabe nagani haka tariko hannuta suka, fada cikin bukar zaune yake gaban wata katuwar tukunyar tsafi baki wulik da shi fuskar'shi tamkar ta gwaggo biri idanu shi, jajir masu kama da garwashin wuta ga shi da kiba ciki sa kamar na mai cikin wata tara yana daure da walki na fatar damisa cikin sa, sai walkiya yakeyi kamar wanda yashafa mangyada ya zaro kafirai idanusa yadakawa hajara tsawa cikin muryar'sa mai kama da kukan jaki yace ke zauna da sauri hajara tadawo haiyyaci'nta cikin rawar jiki ta kai zaune.... 🍆🍆🍆MIJIN YAR UWA🍆🍆 TAA🍆🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~1⃣0⃣~ Boka duguzuu dan asarariya ya watsawa mata mugaye idanusa ya bude bakin'sa mai kama da na alade yace meke tafe da ku mata masu neman biyan bukata"? Cikin rawar murya hajara tace boka dama kishiya ta ce ta, takura ni ta hanani rawar gaban hantsi sai zazzaga 'ya'ya takeyi ni ko bata wata bantaba yi ba a taimaka boka a rufe mata mahaifa tadaina haihuwa in kuma da akwai wani taimako da za'a bani nima nasami nawa iri a taimaka min ni dai burina in haihu. Tun lokacin da tafara magana boka duguzuu yake kallon ta gani ta dasa aya a zanceta yasa bude katon bakin'sa wani kafiri wari mai kama da mushi kare ya buge fuskar Hajara yace angama bukatar'ki za ta biya aljana barahazaa" za ta biya miki bukatar'ki yadaga hannu'shi sama yasoma surutu da wani yare, shi kan'shi in aka tsure shi, ba zai iya fassara abunda yake cewa ba sai ga wata 'yar tukunya laka tafado cikin tafin hannu shi ya mikawa hajara yace kije ki binne ta kada ki bari wani, ido yagane ki kuma karki binne ta inda za'a iya hako ta indan ki kayi haka har abada sadeeya ba za ta kara haihuwa ba amma kuma duk ranar'da aka hako ta zan sadaukar da mahaifa ki ga aljani qudulu. Jikin hajara yafara rawa boka duguzuu yakara dauko wata robar mai dauke da wasu ruwa yace wannan kuma ki shanye da kin shanye su za ki Sami ciki ki zube duk, kudin da ke cikin jikkar ki hajara ta zuge "zip" din "handbag" dinta tafito da dubu dari biyu ta ajiyewa boka duguzuu cikin hargowa boka duguzuu yace ke baqar ja'ira sauran dubu dari da ki ka bari cikin jikkar ubanki za ki siyawa goro da su"? Maza ki ajiye min kudina ku bace min da gani da sauri hajara ta ajiye ragowar kudin suka fice daga cikin bukar. Duk yadda boka ya umurce hajara tayi ta aiwatar bayan wata uku sai ga hajara da ciki "woho-woho" hajara tamkar za tayi hauka sai takara bude shafi na iskanci tana yiwa sadeeya habaici bayan wata tara ta haife 'ya mace saidai hajara ba haka taso ba saboda namiji taso ta haifa, ranar suna aka radawa "baby suna Na'eema..... 🖊excellent writer's🖊 Jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:29 am] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆🍆MIJIN YAR UWA TAA🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~1⃣1⃣~ Hajara sai farin ciki takeyi sakamako gani sadeeya ta, share shekara takwas bata kara haihuwa ba, Amar da Na'eema sun shaku da junan su amar yana matukar sonta a, lokacin akayi auren hafsat kwatsan sai ga ciki ya baiyana a jikin sadeeya abinda yayi matukar girgiza hajara ta banzama wurin boka duguzuu, tun dawowar ta daga wurin boka duguzuu take kukan baqin ciki saboda boka yace aiki da yayi mata ya lalace kuma aljani dugulu ya cinye mahaifarta, duk yanda hajara taso ta zubar'da ciki sadeeya saidai "Allah bai nufi ciki da zubewa ba saida cikin sadeeya yayi watani goma chib sannan ta haifi 'yar ta kyakyawar gaske tun ranar suna aka radawa baby suna Raheela hajja Rahee na tsananin son raheela tun tana jinjira, bacci kadai ke raba ta da Raheela lokacin da raheela ta esa yaye hajja Rahee ta yaye ta tun daga lokacin rikon ta yakoma wurin ta dalili dayasa raheela ta tashi a sagarce, ta kuma hinjire bataji magana kowa, bata tsoron ko ta kwana balle ta tashi duk inda ake neman fitsarariya yarinya in aka kawo wurin Raheela dole a shafa fatiha lokacin da raheela ta kai shekara 13 a duniya tsiwa da fitsarar ta suka kara baiyana, tun daga yanayi maganar'ta za ka gano lallai wannan goyon kaka ce nazeer da na'eema suna matukar son raheela duk abinda za tayi sam basa gani laifin ta, saidai ma su goya mata baya raheela sai sheka iya shegen takeyi kuma ba wanda ya esa yayi mata magana hajja kaaka ta wanke masa allon sa wannan yakara ba raheela dama tacigaba da tsula tsiya son ranta raheela ,na cikin ganiyar sheka iya shege'nta yaa Amar yadira kasar 9ja wanda ya share tsawon shekaru bakwai a kasar Germany" yana karatun "medicine" dawowar Amar su mamee suka sami sauki iya shegen'ta saboda Amar lakada mata dan banza duka yakeyi, wannan yajanyo kiyayya zazzafa tsananin su, Amar ya tsani raheela haka ita ma ta tsane shi matukar Amar ya hadu da raheela sai ya dake ta..... 🍆🍆🍆MIJIN YAR UWA TAA🍆🍆🍆🍆 💕love story2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~1⃣2⃣~ AMDAWO LABARI******* Raheela zaune tasaka "plate din abincin gaba tana kuka har wani shure-shure kafafu takeyi kaaka tana gefen tana sallah cikin shashekar kuka raheela tace na rantse yau ba zan ci abinci nan shine don tsohon wulakanci irin na umma hajara za ta saka kifi a miya bayan tasan banaso kifi kaaka ki gama sallah muje tafadi dalili da yasa tayi amfani da kifi Amar da ke tsaye bakin kofa yana kallon iskanci da raheela takeyi yaja tsoki yakarasa shiga dakin yasake mata rankwashi aka a firgice tadago idanuta tana kallon Amar tana shafa kan'ta yasaka kafar'sa yayi "ball" da ita goshin'ta yabuge gefen gado wani masifafe ihu na azaba tasaki ya rufe ta da duka sai ihu kiran sunan kaaka takeyi. Kaaka na sallame sallah ko addu'a batayi ba ta mike tanufi Amar da ke ta faman jifgar raheela tasoma kachaniyar kwatar raheela daga hannu shi, gani yaki yasaketa yasa kaaka ta gantsara masa cizo a hannu ae kuwa ba shari yasaki raheela yasoma yarfe hannu'shi yana kallon fuskar kaaka, yace kaaka yanzu don nadake wannan fitinaniyar shine za ki cije ni"? Kaaka ta galla masa harara tace matukar baka daina sauke hannu ka akan Raheela abinda yafi cizo ma zan iya aikata maka kai kenan kullum cikin dukan yarinya haka ko dazu kafasa mata baki, wannan ae zalunci ne da mugunta in har karfi ka ke takama da shi kaje waje kanemi tsara ka amar ya tabe baki, daga bisani yace ina tausaya miki kaaka lokacin da za ki fara karatun littafin danasani akan wannan turba ta sagarci da tabarbarewar tarbiya da ki ke doura Raheela akai 'ke kenan kullum cikin haushi da hayagaga akan wannan gantalalleliya yarinya cikin zafin zuciya kaaka tace yanzu don iskanci da wulakanci irin naka, amar za ka dubi tsabar ido na kace ina haushi ni kare ce da dinga haushi"? wannan shine, kashedi na karshe da zan kara yi ma akan Raheela ba ruwanka da abinda takeyi saboda ba'a karkashen ikon ka take ba Amar yaja tsoki cikin konar zuciya yafice, daga dakin kaaka tabishi da zagi daga bisani ta koma wurin Raheela da ke durkushe tana shashekar kuka..... 🖊excellent writer's🖊 Jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:29 am] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆🍆MIJIN YAR UWA TAA🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~1⃣3⃣~ Kaaka ta dagota tace maza share hawaye ki, Allah sai yasaka miki ita kuma hajara za ta hadu da fushi na don sai naci mutunci ta sai, tafada min dalili da yasa tasanya kifi a miya bayan tasan bakyaso raheela ta turo baki tace, kaaka wallahi na tsani yaa amar da umm Hajara da zan sami aron bindiga da sai na halbe su. Na'eema tayi sallama takarasa shigowa cikin dakin fuskar ta dauke da Murmushi, tace laifi me yaa Amar da umma'naa sukayi da raheela za ta halbe su"? raheela ta murguda baki tace saboda duk gidanan su kadai ne suke duka na, na'eema tayi dariya tace "Allah ya huce zuciyar raheela ta hajja kaaka masu yi ba'a fadi hankaka maida 'da wani naki turnuku fada ibilissai yaro bai gani ba balle raba" kaaka tayi karaf takarasawa na'eema ta hanyar cewa wane shi, dan ubansa kuma kijawa hajara kunne hawaiyar'ta taki yaye rama ta naga alamar tanaso nayi mata kidin zari irin wanda tun lokacin da lami ta haife ta ba'a taba yi mata irin sa ba. Na'eema ta bata fuska tace haba kaaka wannan wane irin yanka kauna ne"? Ae ko don albarkaci na yaci ace kin ragawa umma" ni kenan kullum manne a dakin'ki kina ci mini fuska ta hanyar zagin mahaifiya taa. Kaaka ta galla mata harara tace dama barewa ba za tayi gudu ba 'da ta yayi rerafe raheela da gidan ubanta amma, masifa da bala'e da kuma mugun alkaba'e da hajara takeyi mata yasa tadaina shiga bangare ku. Na'eema ta cire hijab dinta ta nufi "bathroom" tana cewa ae sai kiyi ni ba zan iya wannan tashin hankali ba ke kenan kullum cikin masifa bakin'ki ko ciwo ba yayi. Kaaka tace masifa na chan tare da hajara kuma, yadda bataso haka za tacigaba da gani saidai hasada da baqin cikin raheela su zama ajali'nta a shagwabe raheela ta riko hannu kaaka tace kiyi shiru haka nan kaaka kaina yafara ciwo da sauri kaaka ta riko kan'ta tafara yi mata tofi.. WASHE GARI****** Da yamma Amar Yana zaune bisa farar kujerar roba a "compound" din gida hannu shi, rike da "newspaper" ta dailytrust" yana dubawa da karfi yaji an bude kofar shigowa cikin gidan yadago idanushi ya mayarda hankali shi a bakin "gate" raheela ya gani taja birki sai faman haki takeyi, ga wata uwar damara da taci da hijab din'ta kanta babu dan kwali'n jela gashinta sai reto takeyi a bayan'ta amar ya yafito ta da hannu'shi nan take tafara bubuga kafafu a kasa yatsu shi uku yadaga mata alamar in ya kirga uku bata zo ba tasan sauran, da gudu takarasa wurin sa ta marairaice murya kamar mutuniyar kirki tace dan Allah yaa Amar kayi hakuri na rantsi ba wanda na tsokana, kayi hakuri karka dake ni kalli baki na da goshi na duka da kayi min jiya ne ko warke, banyi ba. Wani mugun kallo yaa Amar ya watsa mata ya kuma daka mata tsawa ta hanyar, cewa "shut up stupid girl"? Da sauri Raheela ta rufe bakin'ta da tafin hannuta sai wani zare idanu takeyi yakara daka mata tsawa yace oya kiyi "kneel down" raheela ta zube gaban shi yaa Amar ya tsura, mata idanu da sauri Raheela ta kawar'da fuskarta tace ni kadaina kallo na da idanu ka na "horrors" Ko so ka keyi nayi mafalki ka takarasa magana hade da murguda baki. Yaa Amar yayi shiru kamar mai nazari daga bisani yace raheela yanzu don bakida kunya za Ki danganta ni da "horror"? Turo baki tayi tace to ae ni yaa Amar ba karya nafada ba kowa "eye's ball" dinshi " black ne amma banda kai. Yaa amar ya galla mata harara yace ke munafuka nawa wane irin colour ne? Yatsine fuska tayi daga bisani tace "sky blue" yaa amar yayi murmushi, yace umhh.. Da sauri Raheela tace yaa Amar daga kan'ka sama kagani zaro idanu yayi yace me zan gani"? Tace kadaga zan nuna maka "something very important" yaa Amar ya yatsine fuska yace in nadaga banga komai ba sai na fanfalla miki mari yakarasa zance sa hade da daga kai sama raheela tace yaa amar kaga yanda giragizai suke "sky blue" haka ma "eye's ball" dinka yake wani wawa tsoki yaa amar yaja ya sake mata rankwashi a gigice raheela ta dafe kai, yace ina dan kwali'n ki"?da kyar tace yana ciki yace kodai kin jefar da shi wurin dambe"? Ta girgiza kai yace tashi ki bace min da gani ta mike tsaye tanufi bangare su "direct" bedroom din Anty amarya ta wuce da yake haka suke kiran sadeeya jin karar ruwa a "bathroom" yasa tayi kwanciyar ta bisa gado Anty amarya na fitowa daga "bathroom" tayi 4 eye's da raheela ta murtuke fuska tace ke lafiya me yashigo da ke nan"? Raheela ta mike zaune tace zuwa nayi naganki, Anty amarya ta galla mata harara tace kidai zo daukar magana wurin hajara raheela ta girgiza kai hade da cewa ni ba wuri'nta na zo ba Anty amarya ta tabe baki tace banaso fitina raheela nasan halinki sarai baza ki fita bangare nan ba batare da kin tsokani hajara ba don haka, tashi ki koma bangare ku raheela ta fashe da kuka cikin shashekar kuka tace me, nayi miki Anty amarya duk lokacin da nazo wuri'nki kidinga korata sai kace bake ki ka haife ni ba batare da ta jira amsar da Anty amarya za ta bata ba ta fice daga dakin a babba falon gidan taci karo da umma hajara zaune ko kallota raheela, bata yi ba kaitsaye ta nufi kofar fita hajara ta bushe da dariya tace yau kuma waya taba uwar rigimamu take kuka harda su majina a fuska"? Raheela taja birki hade da juyawa ta watsawa hajara harara ta kuma ja mata tsoki tace ba'a saniba, hajara tace to gantalalleliya 'yar gadon mugun abun fitsara za kiyi min" Raheela ta murguda baki tace eh' anyi miki fitsara kiyi duk abunda za ki iya hajara tace watakila sata ki kayi, akayi miki duka shine ki ke kuka raheela tace "Allah ya esa ban yafe miki ba tunda ki ka yi min sharri sata, hajara tace ae raheela sata gadon ta ki kayi waye bai san buzaye da sata kamar gafiya. Raheela takara harzuka da jin furucin umma hajara tace ke ma ae kina sata don kin taba yiwa Abba naa sata har kaaka tace wurin bokaye za ki kai kudi Allah yatoni asiri ki...... 🍆🍆🍆MIJIN YAR UWA TAA🍆🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~1⃣4⃣~ Hajara tayi kukan kura ta nufi raheela da gudu raheela takarasa ficewa daga falon, hajara tafara zage-zage kamar mahaukaciya, shegiya tabataciya, yarinya haka zaki qare a gantale matukar ina numfashi a doron duniya bake ba aure sai na mayar'da ke abar kwatance, Anty amarya da ke sallah ta sallame tasoma lazimi daga bisani tadaga hannaye ta sama tasoma nemawa 'yarta kariya daga ubangiji talikai. Raheela na fitowa taci karo da nazeer ihu tasaki tana shafar goshin'ta da ya buge kan nazeer. Nazeer yadago yace "oh shirt" raheela tace "oh no" suka kara hada baki sukace "oh yes" hannu yabata suka tafa dama wannan shine dabi'ar su da kyar nazeer da raheela su hadu basuyi wannan abun ba nazeer yace haba tawan wai sai yaushe za kiyi hankali kidaina wannan gudun naki na fanfalaqi"? Raheela ta harara shi tace sai ranar'da kayi hankali nima zan yi saboda ni da kai jirgi daya ya kwaso mu nazeer yace karya ne, wallahi nafiki hankali da natsuwa raheela tace mu je a tambaye kaaka tafadi wanda yafi hankali tsakani ni da kai, nazeer ya kyakyace da dariya yace, wayo ki keso kiyi min koh"? Saboda kinsan kaka za ta goyi bayan'ki raheela tayi murmushi, tace ba wani wayo kawai dai nafika hankali da wannan dogon sarhi suka karasa bangare kaaka. Haka rayuwar raheela tacigaba da tafiya a karkace duk lokacin da daddy yayi yiwa kaka, magana akan tadaina shagwaba raheela sai ta aza kuka wannan yasa "daddy yadaina magana dama shi, abba abdullah ba magana yake yi ba yaa Amar ne kadai yake da jarunta dukan raheela a zaune lafiya tun kaka na kai kara shi wurin mamee har tagaji tadaina saidai duk lokacin da yadaki raheela tayi mishi Allah ya esa. BAYAN SHEKARA UKU***** Raheela an zama 'yan mata hankali da natsuwa sun yafara shigarta a lokacin tana shekarar karshe a secondary school" na'eema kuma ta kamalla "degree dinta.. 🖊excellent writer's🖊 Jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:29 am] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~1⃣5⃣~ Note:- sharhi akan masu yada maganganu akaina kuna cewa buk din MIJIN YAYA TAA babu komai cikin sa sai batsa da badala to kusani ba ni nake rubuta shi ba, suna buk din'mu ne yazo daya Shiyasa na chanzawa nawa suna zuwa MIJIN 'YAR UWA TAA ynz kuma yarage naku sai kuje ku zagi NBABA MADA saboda shine yake rubuta mijin yaya ta mai batsa kuma kusani duk wanda, yakira baby amrah ya zagi ta shi da Allah kuma bata yafe ba sai Allah yayi mata mumuna sakayya akan'shi masoya na da suka dinga kare ni na gode Allah yasaka da alkhairi makiyya na da suka dinga zagi na da yada maganganu marasa kyau akaina kuma na gode Allah yasaka da alkhairi. Lurv u oll my fans😍 Alhaji Abdullah zaune a falon shi, umma hajara na gefen sa ta wani hakince ita a dole ga uwargida anty amarya tana zaune bisa "one star" da ke facing" dinsu raheela da na'eema suka shigo suna rike da hannu juna kaitsaye raheela ta nufi wurin alhaji Abdullah cikin shagwaba ta zauna bisa hannu kujerar da yake zaune a kai hannu ta rike da "Swéet din lollipop" tana tsotsa sai kace 'yar yaye umma hajara ta watsa mata harara hade da cewa to fitsarariya uwar 'yan fitsara ke kinfin karfin zama kasa ne"? Raheela ta yatsine fuska tacigaba da tsotsan "lollipop dinta tana kada kai alamar rashin mutuncin'ta nason motsawa, aunty amarya tadaka mata tsawa tace ke bada ke ake magana ba da ki ka wani shantake"? Maza ki sauko kasa raheela ta turo baki ta zauna kasa alhaji abdullah yayi murmushin, yace banaso kuna takurawa mama'naa ku bar'ta tayi abunda takeso kurciya ce kawai take damunta wata rana kamar batayi ba. Umma hajara tasaki kalma shahada harda su tafa hannu tace kai abdullahi ka ji tsoron "Allah yanzu wannan katuwar baliga za ka danganta, ta da kurciya Allah na tuba wannan da a kauye take har ta wuce muzalin aure. Raheela ta kyabe baki tace kai umma harda su kalma shahada sai kace kinga macijin, kuma ki daina kiran suna abba na bakatatan ba ko dan lakabi umma hajara ta galla mata harara kamar kwayar idon'ta yafado kasa tace to iyani mai dan doro shi uban naki baiyi korafi akaina ba sai ke shugaba ta marasa kunya gani yadda umma ta zakalkale tana kunfar baki yasa abba yataka mata birki ta hanyar cewa kefa hajara bakida ta natsuwa miye na biyewa Maama kina tada jijiyoyi wuya da 'yar cikin'ki wannan ae hauka ne. Aunty amarya tace amma abban na'eema ita ma kan'ta maama ba kanwa lasa bace a wasu lokuta itace ummul-aba'esi tsokano fitina a gidanan. Abba yaja tsoki daga bisani yace ku dai kawai kun aza mata karan tsana, dalilin da yasa bataso shigowa "side" dinan ya juya wurin Raheela yace mama'naa ki dinga hankuri da su kinji koh"? Raheela tayi murmushi, hade da cewa toh..abba ta fakace idanu mutane falon ta yiwa hajara gwalo, hajara takara harzuka ta kuma kudiri anniya ko ta wane hali sai, ta tarwatsa rayuwar raheela. Abba yayi gyaran murya daga bisani yace dalilin da yasa na aika kiran'ku saboda ke ne na'eema kin kamalla karatu'nki lafiya kuma cikin nassara don haka nabaki wata biyu kacal, kifito da mijin aure ni da yaya mu yanke shawara a hade bikin aure ki da na su Abdul ayi a lokacin daya, shima amar da yazo "weekend" dole yafito da mata ko mu aura masa zabi mu, rass...gaban na'eema yafadi numfashi'nta yadinga fita da sauri-sauri wani masifafe gumi ya tsiyayo akan goshin'ta yasauka bisa fuskar'ta, da kyar ta tattara raguwar natsuwa ta tasoma share gumi da gefen hijab dinta, abba yacigaba da cewa lamari Amar yafara tsorata ni ace matsayin shekaru shi bashida budurwa"? Aunty amarya tayi murmushin, tace miye abin tsoro abba na'eema"? in la'akari da miskilaci irin na amar zai yu akwai wanda yakeso fada ne kawai baiyi ba raheela tayi karaf ta karbe zance hanyar cewa abba yaa amar bakin jini ne da shi kullum fuskar'shi a hade kamar maigadin makabarta ta ya za'ayi yasami budurwa kawai ku hada shi aure da lantana mai aikin mamee za suyi matukar dacewa da juna takarasa zanceta tana washe hakora. Abba ya kyakyace da dariya yace kai mama'naa wallahi bakida dama ke da Amar bansan ranar'da za ku shirya ba, raheela ta turo baki tace babu ranar abba saboda yaa Amar mugu ne duk lokacin yazo weekend" hankali shi ba zai kwanta ba har sai yasakani kuka nima shiyasa bana son'shi. Abba yakara tintsirewa da dariya umma hajara sai harara take galla mata, aunty amarya kuma sai murmushin takeyi sabani na'eema da ta tsunduma a kogin tunani da neman mafita, abba ya tsagaita da dariya da yakeyi yace kamata yayi maama na hadaki aure da Amar, raheela ta zabura hade da zaro idanu kamar wanda taga abin tsoro daga bisani tace "Allah tsare gatari da sarar shuka ko da gida da mota, makka duk shekara abba za ka bani ba abinda zanyi da yaa amar nifa abba na tsani yaa amar " I hate him more than my own death" Aunty amarya ta daka mata tsawa ta,hanyar cewa ke dallah rufewa mutane bakin'ki in aka kyale ki sai ki wuce makadi da rawa tashi ki koma inda ki kafito raheela ta mike tsaye tayi kasa da murya tace abba ni yaya nazee nakeso, kuma shi za ka aura min kaji abba"? Abba yayi dariya yace wannan hadin shi ake kira da gwado, nazeer da raheela a matsayin mata da miji lallai za'a tafka tsiya raheela ta bata fuska cikin shagwaba tace Allah abba yaya nazee yana da hankali kuma y.....umma hajara ta katsi mata hanzari tace ke dallah kifita kibamu wuri, duk kinbi kincika mana kunne da shirme ki na banza da wofi raheela ta juya tanufi kofar fita daga falon takara juyowa karaf suka hada ido da umma hajara ta murguda mata baki umma ta zaro idanu tace raheela ni ki ke murgudawa baki"? Da gudu raheela takarasa ficewa daga falon, "direct" ta wuce "side" din mamee... 🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~1⃣6⃣~ Tana shiga falon mamee tafara kwada sallama sai kace bakuwa, jin ba'a amsa mata ba yasa taja tayi tsaye wani fitinane kamshi takeji yana fitowa daga "kitchen din mamee yasa babu shiri ta nufi "kitchen" din gani wanda ke ciki yasa tafara sanda tana karasawa kusa da ita tace ke a firgice lantana ta kurma ihu raheela ta tintsire da dariya tace ke dai lantana kin cika tsoro, lantana taja dan karami'n tsoki hade da cewa ke kuma kin cika daukar alhaki. Raheela ta zaro manya idanuta tace kai'kai lantana baqi za'ayi ne"? Lantana tace me ki ka gani ne"? Raheela ta yatsine fuska tace naga kina soya 'yan uban kaji duk kin cika gida da kamshi, lantana ta washe hakora hade cewa kin manta gobe juma'atu babbar rana likita zai dawo"? Raheela taja tsoki tace aiki'n banza da wofi yanzu duk 'yan uban soyayu kaji nan saboda yaa amar aka tanadi su"? Lantana tace kwarai kuwa raheela takara jan tsoki ta mika hannu cikin katuwar "food flask" din da kaji'n suke ciki tadauki cinya nan take ta cinye ta jefar'da kashi takara daukar wata cinya tace mutumi da sai gobe zai dawo shine don tsabar rawar jiki ake soya masa kaji tun yau dole gobe yaci dumame lantana tace ae likita baya cin soyayar kaza sai ta kwana raheela tabe baki tace yaa amar badai iya yi ba takara daukar cinya lantana riko hannuta tace dan Allah ki rufa min asiri kada yaya na'eema tace na cinyewa likita, kaji mtwww....raheela taja tsoki tace dallah sake ni duk yawan kaji nan ace na mutum daya ne wannan son kai har ina wallahi dole na yagi rabona na'eema ce tashigo cikin "kitchen din tace kefa raheela bakida kirki an gaya miki na banza ne da za ki yagi rabon'ki"? Raheela tace na banza ne mana tunda ba da kudi'nki ki ka siya ba haka kawai za'a dinga kwasowa daddy kaji gona ana soyawa kato na'eema ta galla mata harara hade da cewa yaa amar ne Kato"? Kafin raheela tabata amsa mamee tashigo, "kitchen tace wai hayaniya me nakeji haka"? Raheela tace mamee yaya na'eema ce wai ba za ta sami naman kaza nan ba kuma ka gashi yabiya min a rai, na'eema ta zaro idanu tace Allah mamee koda nashigo "kitchen dinan da katuwar cinya a hannu'ta mamee tayi murmushin, tace yi hakuri na'eema ki kara mata kadan ki huta da fitina ta na'eema tadauko fifike ta mikawa raheela a yatsine raheela take kallon fifike'n tace Allah ya kiyaye naci fifike kaza badai naman na yaa amar ne a gaban ki za mu ci, shi tare na'eema tayi dariya tace ke da wa raheela"? Raheela ta turo baki hade da cewa ni da yaa amar na'eema takara tintsirewa da dariya nima da zanyi farin Ciki in haka takasance mtwww...tayi tsoki ta fice daga cikin "kitchen din... 🖊excellent writer's🖊 Jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:31 am] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~1⃣7⃣~ WASHE GARI******* Tun da misali karfe 11:00am na'eema tashiga kitchen" tafara hadawa yaa amar hadade girki, tuni kamshi yacika gida mamee tafito daga "bedroom" dinta tace kai na'eema wannan kamshi har ina tun kafin ki karasa girki nan yawu na sun fara tsinkewa, na'eema ta kyakyace da dariya mamee tacigaba da cewa na fahimce cewa kece ki ke kara shagwaba Amar shiyasa har yanzu yakasa nemawa kan'shi abokiyar zama, kodai 'yar gida za'ayi tsakani ki da Amar"? Na'eema ta rufe fuskarta da tafin hannuta mamee tayi murmushin hade cewa dama najima ina zargin faruwa hakan, daga gani wannan shakuwar taku ke da Amar nasan akwai wani abu a kasa shi, tun lokacin da amar ya koma abuja da aiki nagano manufar ku shi, yakasa fitarda Matar aure, ke kuma kullum cikin korar samari ashe kunsan kulaliya da ku ka kulla, na'eema takara kyalkyalewa da dariya tace kai mamee ni ba abinda ke tsakanin'mu mamee ta rankawashe ta tace karya ki keyi munafuka, indai tayi tsami dole mu ji, mamee na karasa zanceta tafice daga kitchen din. Bayan na'eema ta kamalla girki tayi wanka tana zaune gaban "dressing mirror" sai faman caba "make up" takeyi sai kace sabuwa amarya raheela da ke nade cikin "blanket" tana baccin ta falka tasauke idanuta akan na'eema, ta wani yatsine fuska ta yaye "blanket" tayi mika hade da dogowar hamma, na'eema ta mike tsaye tasoma feshe jikinta da turare "violet roses" raheela sai faman kallon'ta, takeyi daga bisani ta tabe baki tasauko bisa gado ta nufi "bathroom" har ta murda "handling" din kofa ta juya tace iska na wahalar'da mai kayan kara batare da ta jira amsa da na'eema za ta bata ba tashige "bathroom" na'eema tayi murmushin, hade da girgiza kai, ta dauki mayafinta tafice daga dakin. Kaaka na zaune a falon hannuta rike da casbaha na'eema tafito, wani malalacin kallo kaka ta bita da shi, tace ke kuma sai ina"? Na'eema tace ba fita zan yi ba kaka ta zaro ido tace wai na'eema yaushe zaki daina, wahalar'da kanki akan Amar"? Banza tayi da kaka kamar bataji abinda tafada ba, sai ma wayarta tadauko tafara buga "game" kaka tayi dariyar takaici tace matukar za ki cigaba da jiran Amar to kuwa za ki tsofe a gida ne ki yiwa kan'ki fada na'eema ki dangana da wannan jarababe son amar da ki ke yi, jin abunda kaka tafada yasa tadago idanuta ciki'n sanyi murya tace bazan iya ba kaka saboda son yaa amar yariga yayi yiwa zuciyata mumuna illah. Kaka tace yaro, yaro ne yaro man kaza, in banda ke da abinki na'eema wa kika taba gani yayi so shi kadai"? Amar bai masan kinayi ba kibawa kan'ki lafiya ki hakura da shi "Allah zai kawo miki, wanda yafi shi,. Na'eema ta girgiza kai tace bana tunani zan sami wanda yafi yaa amar kaka in har narasa yaa amar tabbas zan rasa rayuwata, kuma na tabbata shima yaa amar yana sona, tun kafin na mallake, hankali kaina yaa Amar yake nuna, min kauna hade da kulawa, karki manta kaka, har gobe yaa Amar yana banbantani da raheela wannan kadai ya esa ya nuna miki yana sona kuma ina ji a jikina yaa Amar yayi kusa furta mini abunda ke zuciya'rshi. Kaka tace umhh...yayi kusa dai yafurta mata, a firgice na'eema ta jefar da wayarta bisa kujera da ke kusa da ita cikin tashin hankali, tace kaka dama yaa amar yataba fada miki akwai wace yakeso"? Kaka tayi yiwa na'eema kallon uku saura kwabo batare da ta tanka mata ba ta mika hannu ta janyo dan karami'n "basket" mai dauke da goro ta bude ashasha ta dauko katon goro farin tass..tasaka a bakin'ta ta gutsira tacigaba da Jan casbaha. Na'eema tasauke ajiyar zuciya tace dan Allah kaka kifada mini wacece yaa amar yakeso"? Kafin kaka tabata amsa raheela tashigo falon kaitsaye ta nufi "two star ta zauna ta mayar'da ganinta wurin na'eema gani yadda take hada gumi yasa tace lafiya yaya na'eema badai fada ki kayi da kaka ba"? Cikin sarkewa halshe na'eema tace a'a. Raheela ta bata fuska tace duk lokacin da naganki cikin wannan yanayi kaka tayi magana yaa Amar, takarasa zanceta hade da Mikewa tsaye ta riko hannu na'eema tace zo mu tafi kyale kaka tana kishi ne don za ki kwance mata miji. Raheela da na'eema suka fice daga falon sukayi "side din mamee suna cikin tafiya raheela tace yaya na'eema zan baki shawara amma takasance sirri a tsakani mu, saboda in kaka taji za ta hana ki na'eema taja birki tana kallon raheela fuskarta dauke da mamaki zance ta..... 🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~1⃣8⃣~ Raheela ta lumshe idanu'ta daga bisani ta bude su cikin sanyaya murya tace me zai hana ki fadawa yaa Amar kina sonshi"? Na'eema tayi shiru kamar me tunani daga bisani tace kina gani wannan shine kadai mafita"? kwarai kuwa yaya na'eema saboda yaa amar shu'umi mutum ne ba kasaifai ake gane inda yadosa, ba ni anawa gani yaa amar yana son'ki kawai girman kai da miskilaci irin nashi sune suka hana shi baiyana soyayya'r da yake miki ki daure ki fada masa abinda yake zuciyar'ki. Tsantsan farin Ciki ya maye gurbi fargaba da ke tare da na'eema ta rungume raheela tace "thanks my little sister" Shiyasa banada wata kawa da ta wuce ki raheela a duk lokacin da nashiga matsala, ke ki bani shawara mai kyau Raheela tayi murmushi hade da cewa banida kamar ki yaya na'eema shiyasa bana farin ciki matukar kina Cikin bakin ciki, kiyi min alqawali za ki baiyanawa yaa Amar sirri da ke zuciyar'ki na'eema ta share hawaye da suka zubo mata tace nayi miki alqawali "my little matukar ina numfashi yau zan yayewa yaa amar hijabi soyayya'r sa da ke lullube da ni, raheela tayi dariya tace da kyau 'yar uwa taa haka nakeso ji. na'eema ta dan murmusa Cikin tsokana tace ina fatar ba ki manta ba yau tare da yaa amar za kiyi lunch"? Raheela ta turo baki tace nafasa" na'eema ta tintsire da dariyar keta harda dafe ciki tace dama ba za ki iya ba cika baki ne kawai Irin naki, raheela ta ture hannu' na'eema daga riko da tayi mata tace Allah kuwa zan iya na'eema ta tsagaita da dariya takeyi tace to kiyi mana nifa har za ki ci abinci tare da yaa amar, komai ki keso matukar bai fi karfi na ba zan mallaka miki shi, a matsayin kyauta ta nuna bajinta hade da gwazo da ki kayi ta karasa zanceta cikin dariya. Raheela ta tabe baki, tace material" din da yaa Amar ya kawo miki "last week" shi nakeso, na'eema takara kwashewa da dariya daga bisani tace dama tun ranar'da yabani shi naga kina misi-misi da kirar ido nagano cewa kina son "material din kuma na amince zan baki shi amma fa a bisa sharadi sai kinci abinci tare da yaa amar" Raheela ta washe hakora tace shikenan za ki sha kallo yau, na'eema tace uhmm...lallai kuwa yau don jikin wata zai gaya mata kallon sai na baki mamaki raheela tayi mata da wannan "drama" suka shiga cikin gida. Misali karfe 3:20pm raheela na zaune a "parking space"bisa farar kujerar roba Jin da tayi anyi "horn" yasa ta mayar'da hankali'nta bakin "gate" maigadi ya bude gate wata tsadadiyar mota ce kirar "Lexus 2016 model" black colour" sai shaki takeyi, tadanno kai da sauri raheela ta finciko dan kwali'n kanta ta lullube fuskar'ta ta wani langwabe, sai kayi tunani baccin takeyi yaa amar yayi "parking din Motar'shi daga bisani yafito yana sanya da "dark blue din "coat" idanu shi na rufe da farin gilashi ya bude "seat din baya yafito da "briefcase dinshi ya rataya bisa kafada karaf idanu shi suka sauka bisa raheela da ke lullube kallo daya yayi mata yagano ko wacece tabe baki yayi batare da ya tanka mata ba yaraba ta gefenta ya wuce har yayi tako uku yajuyo da sauri ya nufi wurinta, yayi tsaye yana kare mata kallo raheela da ke kallon'shi ta cikin dan kwali'nta tasaki murmushin samun nassara. Mtsww.....yaa amar yaja tsoki yadaka mata tsawa yace ke...a firgice ta cire dan kwali'n da ta rufe fuskarta da shi, me ki keyi anan"? Sannu da zuwa yaa Amar" Yaa Amar ya bude baki yana kallon'ta kasa hankuri yayi yace babbar magana lallai raheela kinfara hankali, raheela tayi murmushi hade da cewa dama chan ina da hankali kaine baka lura da hakan ba. Yaa Amar yakara tabe baki yace uhmm...wannan daba da ki ka kafa anan ta menene ina fatar ba wani sharri ki ke yunkuri kulawa ba"? Raheela ta girgiza kai kamar mumina tace banida lafiya" Me ke damun'ki"? Ciwon kai da jiri" Yaa Amar yayi murmushi hade da cewa don bakida lafiya shine ki zo nan ki zauna" tashi ki shiga cikin gida babu musu raheela ta mike tsaye. Har sunyi kusan shiga cikin gida yakara watsa mata tambaya kin sha magani"? Girgiza kai tayi, ya bata fuska yace miyasa"? Tace banaso magani ya galla mata harara hade da mika mata "keys din dakin'shi yace kije dakina ki jira ni dole kisha magani ko nayi miki allura, cikin sarkewa halshe raheela tace yaa amar banaso allura amma zan sha magani, batare da ya tanka mata ba yakara mika mata "briefcase dinshi ya shige cikin gida. Raheela ta bude falon yaa amar tashiga tayi kwanciyar'ta bisa "three star" ta juya wurin "food flasks din na'eema ta jera ta wani ja tsoki tace kalle duk yawan "food flasks" dinan antanade su ne don mutum daya kai amma yaya na'eema wahalaliya ce. Shigowar yaa amar ce ta katsiwa Raheela tsoki burutsu da take yi, kaitsaye yanufi "bedroom dinshi bai wani jima ba yafito da "panadol extra a hannu'shi ya mikawa raheela ta karba ya cire "coat dinshi ya ajiye bisa hannu kujera yayi yakara cire "white shirt ya yarage daga shi sai "white vest" ya nufi "fridge ya bude yadauko robar ruwan "eva yakara mikawa raheela da ke ta faman aikin kallon'shi.. 🖊excellent writer's🖊 Jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:32 am] Jeeddah Aliyu🌹: ￿￿￿￿🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆￿￿ ￿💕love story 2016￿💕 Na Hauwa Shehu Aliyu￿🌹 ~￿1⃣9⃣￿~ Raheela ta karbi robar ruwan ta ajiye bisa "stool" yaa amar ya zaro mata idanu yace, miye na ajiye ruwa kina nufi bazaki sha magani ba"? Ta turo dan karami'n bakin'ta,cikin shagwaba tace ni yunwa nakeji" Yaa amar yayi shiru yana mata kallon kasan ido shi kadai yasan abinda yakeji game da raheela anyya kuwa zan iya cigaba da boyewa raheela tsantsan so da nakeyi mata har sai ta cika 18yrs"? tambayar da amar yake yiwa zuciya'rshi kenan. Raheela ta murguda baki hade da cewa ni dai yaa amar kadaina yi min, irin wannan kallon" Amar yayi murmushi'n har saida kumatu sa suka lotsa{dimple} tsananin kyau da kwarjini sa suka baiyana ya shafi sumar kanshi ya nufi wurin Raheela da sauri ta kawarda fuskarta, ya durkusawa gaban'ta yayi tagumi yana kallon'ta fuskar'shi dauke da tsadade murmushi'n raheela na juyo suka hada ido yadaga mata gira da sauri raheela ta janye kafafu'ta ta aja su bisa kujera da take zaune, ta rungume hannaye ta bisa kirji'nta yanayi ta tamkar na mai jin sanyi. Amar yayi kasa da murya yace miyasa ki ke son zama da yunwa raheela"? Raheela ta runtsa idanuta sakamako wani masifafe sanyi da ke ratsa "bones" din'ta jikin'ta na "shaking kamar wanda "shocking yaja da kyar ta iya bude baki tace miyar kifi akayi ni kuma banaso kifi gani yadda take magana idanuta a rufe yasa yakara cewa to ki bude idanu ki mana kin wani rufe idanu sai kace kinga "horror" ta girgiza kai hade da cewa ba zan iya ba tsoro nakeji" Amar ya hade fuska yace ki bude idanu ki ko na kwawada miki mari babu shiri raheela ta bude idanuta, ta sauke su bisa fuskar'sa yayida shi kuma ya lumshe nasa daga bisani ya bude su ya mike tsaye, hade da cewa sauko kasa na zuba miki abinci, wani shegen dadi yarufe ta dama abinda takeji jira kenan da sauri ta zauna bisa "center carpet" Amar ya zuba mata "jallof din shinkafa wanda taji 'yan ciki da "carrot da cabbage" ya zuba mata "pepper chickens" a sama ya tura mata "plate gaban'ta raheela ta yatsine fuska tace ba zan iya cinye shi ni kadai saidai mu ci tare batare yace komai ba ya dauki "spoon" yafara cin abinci gani haka yasa ita ma tafara ci suna cin abinci yana wanke'ta da murmushi, ta ajiye "spoon ta wani bata fuska yaa amar yace lafiya ki ka ajiye spoon"? Raheela ta murguda baki hade tace ba kai bane ke sanya ni Jin sanyi, amar ya zaro idanu fuskar'sa dauke da dinbi mamaki yace kamar ya ina sa ki jin sanyi"? Cikin rashin damuwa raheela tace wannan kallon da ka ke yi min, sai kace kana gaban "girl friend dinka tsananin tsoro da firgici suka lullube yaa amar bai ankara ba ya hadiye loma da yasaka a baki ae kuwa ta sarke shi yafara tari babu kau-kautawa idanushi suka kada sukayi jajir, sai faman sannu raheela takeyi masa. Na'eema tayi sallama tashigo falon hannu'ta rike da "jug idanuta suka hasko mata amar na tari raheela na durkushe gabansa tana mishi sannnu da sauri takaraso ta ajiye "jug din hannu'ta ta dauki robar ruwa ta balle murfi ta mikawa Amar ya karba yakafa kai yashanye ruwan tass yajefar da roba ya sauke ajiyar zuciya ya jingina bayan sa a jikin kujera ya lumshe idanu. na'eema ta watsawa raheela harara tace ke wace irin mutum ce"? kina kallon yana tari ko ki bashi ruwa sai wani banza sannu da ki ke masa, raheela tayi Shiru tana kallon na'eema da ke durkushe gaban amar tana masa magana sannu yaa amar a garin yaya ka kware haka"? Amar ya bude jajaye idanusa ya mike tsaye yace zan shiga wanka za ku iya tafiya yajuya yashige "bedroom" da sauri raheela ta mike tanufi kofar fita,na'eema tabi ta da kallon mamaki Daga bisani ita ma ta mara mata baya. "direct" raheela ta wuce "side" din kaka zaune ta tararda kaka tana kallon tashar sunnah tv ta zauna kusa da ita kaka tace ayawo kajin birni daga ina ki ke"? Raheela ta yatsine fuska batare da taba kaka amsa ba ta kwanta tayi matsahi da cinyoyi kaka, ita ma kaka bata ni ta kan'ta ba Saboda tasan hali'n mutuniyar'ta ta. na'eema ce tashigo fuskarta a hade tanemi kujera ta zauna, kaka kalle ta ta watsar tacigaba da kallon raheela ta mika hannu tadauki goro kaka tana ci yaa amar yayi sallama yashigo kaka ta amsa masa hade da cewa likita bokan turai saukar yaushe"? Amar yayi murmushi yace tsohuwa mai ran karfe, kinci lokacin'ki kin ci namu na jikoki ki" kaka to shakiyi kafara koh"? Yaa Amar ya mikaqawa na'eema farar leda yace kanwa taa ga tsaraba'rki cikin jin dadi na'eema ta bude ledar zaro idanu tayi sakamako dalleliya waya da taciro cikin kwali'nta. Na'eema ta washe hakora tace na gode Yaa amar Allah yasaka da alheri" amar yace "ameen kanwataa yajuya wurin raheela da ke ta faman tauna goro da karfi sai wani "kas"kas"kas takeyi yadaka mata tsawa ta hanyar cewa ke bana hanaki cin goro ba"? raheela tacigaba da cin goro ta kamar bataji abinda yafada ba" cikin bacin rai yace da ke nake magana raheela ki ajiye goro nan tun kafin ranki yabaci. Raheela ta tunzire baki ta jefar da goron da ke hannu'ta Amar yace ki tofar da na bakinki, hawaye na zuba akan fuskar'ta ta tofar da goro'n" na'eema tace kaka kin ga sabuwar wayar ta kaka ta kyabe baki tace nagani Allah yasa ki more na'eema ta mike cikin murna da jin dadi tace bari naje na gwadawa su umma batare da tajira amsa da kaka za ta bata tafita. Raheela ta mike da gudu tashige cikin "bedroom din kaka yaa amar yabita da kallo kamar daga sama yaji muryar kaka tana cewa kana bani mamaki amar wannan so ne ko ki kai kenan kullum cikin musgunawa raheela kana farantawa na'eema rai bakajin tsoro kiyayya da raheela takeyi maka tayi tasiri a zuciyarta"? Yayida kaka tacigaba da cewa a yanzu raheela ta mallake hankali kanta tana iya banbanci tsakani so da ki ina ji maka tsoro kada kwaba ka tayi ruwa. Amar yayi murmushi yace karki damu kaka saura lokacin dan kakani na sanar'da raheela sirri zuciyata, mtsww....kaka taja tsoki tace yanzu meye amfani abunda kayi"? Cikin rashin damuwa Amar yace na me"? Kaka tace na siyawa na'eema waya ita kuma ka ki siyo mata, amar yayi murmushi yace wannan ae ba bako bane a wuri'nta saboda ba yau nafara siyawa na'eema abu ban siya mata ba don haka banga abin tashin hankali a ciki'n sa ba. Kaka ta girgiza kai alamar tana tausayawa wannan shirme na amar tace, yanzu kafiso kaga raheela tana kuka koh"? Kuma Kaine sanadi hanata rike waya Amar yace Kaka raheela bataji magana don nace tadaina ci goro shine tayi fushi harda shigewa daki" Kaka tayi murmushi tace ba shine dalilin fushi'nta ba amar yace to me take yiwa fushi kaka"? Kaka tace dakin bako ka ne da bazaka shiga ka tambaye ta ba" amar yayi murmushi ya mike tsaye yanufi dakin kaka... 🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~2⃣0⃣~ Kwance take tayi rigigine bisa gadon kaka sai faman shashekar kuka takeyi, Amar yayi tsaye a bakin kofa yana kallon'ta yayida kuka'nta ke ratsa masa zuciya" cikin tako sa na kasaita yakarasa kusa da ita ya zauna jin motsi mutum kusa da ita yasa tafara magana batare da ta juya ba a tunani ta kaka ce tashigo don ta rarrashe ta cikin murya kuka tace kaka tun ina yarinya yaa Amar ya tsane a lokacin ina tunani don ina da rigima shiyasa baya sona amma a yanzu kaka na girma na kuma daina rashin ji duk da haka yaa amar baya sona me nayi masa da ya tsanani"? Sonta da tausayin'ta suka dira lokacin daya a cikin zuciya amar" jin shiru kaka yayi yawa yasa raheela ta juya don gani abunda kaka ta yiwa shiru "4 eye's tayi da amar da ke zaune yana kallon'ta ta galla masa harara ta kawar'da fuskarta amar yasa hannu yajuyo da fuskarta da sauri ta runtse idanu'ta" chan kasa makoshi Amar yafara magana sai kace mai rada "am so sorry raheela kiyafe min kidaina kallo a matsayin wanda baya so kidinga yi min wanda yafi kowa so da kaunar'ki yakarasa zance sa hade da jan karan hancin'ta, raheela ta ture buge masa hannu tace ni ka kyale ni ko yanzu ka bawa yaya na'eema waya ni baka bani ba in kuma aka bani ka karbe katuwar budurwa da ni ace banida waya saidai nayi, amfani da ta kaka. Amar yasaki baki da hanci yana kallon raheela daga bisani yace budurwa raheela yanzu kece katuwar budurwa yakarasa zance sa yana dariya. raheela ta murguda masa baki tace ni dai za ka siya mini koh"? Amar yayi mata kallon kasa ido hade da cewa ba yanzu ba sai kin kamalla "secondary school" Raheela ta bata fuska kamar za tayi kuka tace ka rike kayan'ka banaso, amar ya make kafada alamar "I don't care" ya mike tsaye yasaka hannu cikin aljihu "black jeans" din da ke jikinsa yafito da dan karami'n zobe sai shaki da daukar ido yakeyi, ya riko hannu raheela ya zira mata zobe a dan yatsa ta na hagu yace raheela wannan zobe shine tsabar'ki. Raheela ta tsurawa zobe mai dauke da zane "heart" idanu haushi da takaici suka turnuke ta tace me zanyi da wannan karfe'n"? Amar yace waya gaya miki karfe ne"? Raheela tace ga Abu nan yana kyali dagani sa kasan karfe ne tacire zobe ta mika masa karbe kayan'ka in baso ka keyi na jefa shi a "fish pond" din daddy kafiye su hadiye shi ta karasa magana tana murguda baki cikin zafin rai amar yafinciko hannu'ta da karfi yace..... 🖊excellent writer's🖊 jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:33 am] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕￿love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~￿2⃣1⃣￿~ Yace bakida hankali raheela zuciya'r tawa za ki jefawa kifiye"? Raheela ta tabe, baki tace zobe karfe ne zuciyar'ka"? Matsi mata baki yayi tasaki 'karar azaba hade da cewa washhh.....Yaa Amar da zafi yasaka hannusa sa na dama yadago fuskarta yanuna mata Dan yatsa shi, na hagu idanu'ta suka sauka bisa zobe da ke hannu shi "exactly" irin na hannuta banbanci kawai nashi yafi nata girma ta dan zaro ido tace Yaa Amar wannan wane irin zobe ne yafiye kyali da yawa"? Amar yayi murmushi, yafi fuskarta da dan yatsa sa Yace zobe alqawali ne raheela daga yau, ba za mu Kara fada ba zan mu kasance a tare har karshen rayuwa'r mu. Raheela ta turo baki tace me wannan zance naka yake nufi yaa amar"? Amar ya tabe baki yace oho" Tace to sake ni naji kaka tafara kira na watakila akwai abunda takeso nayi mata, a maimakon yasake ta sai yakara matsi mata baki, ta runtse idanu tace in baka sakeni ba zan kira maka kaka, amar yayi murmushi yace Ki kira'ta mana an gaya miki ina tsoro'nta ne" raheela ta bude idanuta tace ni dai kasake ni please" Zan sakeki amma sai kinyi min alqawali, ba za ki jefar'da wannan zobe ba nayi maka alqawali yaa Amar zan cigaba da kasancewa da wannan zobe'n karfe har karshen rayuwa'ta, amar yayi murmushi hade da cewa "thanks my raheela yasake ta da gudu tafita daga dakin amar ya shafi sumar kanshi yace ina son'ki raheela "I can't do without you" raheela nashiga falon" kaka tadago tana kallon'ta da sauri raheela ta kawar'da fuskarta kaka tayi murmushi, amar yafito daga cikin dakin hannaye sa zube cikin aljihu wando sa shima da kallo kaka ta bishi shi, gani kallon da takeyi masa yayi yawa yasa yace kaka in akwai fura a dama mini zan sha ajima batare yajira amsa da kaka za ta bashi ba fice daga falon. {DARE}******** Da misali karfe 8:30pm Raheela na zaune a falon kaka tana kallon tashar Zee world na'eema tashigo babu walwala akan fuskar'ta ta nemi kujera ta zauna raheela tayi mata kallo daya ta kauda fuska yayida na'eema tasauke ajiyar zuciya tace raheela" shiru tayi kamar ba zata amsa ba daga bisani tace na'am" na'eema tacigaba da cewa ina cikin matsala narasa yadda zan tunkari yaa amar na fada masa ina sonshi wallahi kunya nakeyi kuma ina jin tsoro kada yace akwai wace yakeso inda haka ta kasance ina zan saka kaina raheelat"? Tun lokacin da fara dogon sharhi ta raheela ta tsura zuba mata na mujiya gani ta dasa aya a zanceta yasa raheela ta gyara zama ta kuma yi, kasa da murya kamar munafuka tace ki natsu yaya na'eema ki nemowa kan'ki abunda ki keso in ki ka kuskure yaa Amar ya kubuce miki bana tunani zai dawo gareki. Na'eema takara shiga cikin rudani hade da neman mafita, tace raheela ko za ki fada masa"? Da karfi raheela tace ni kuma"? Ina wallahi ba zan fada ba so ki keyi ya yanka ni"? kedai da Allah yadaurawa jarabar sonshi ke ce za ki fada masa da bakin'ki ae waka a bakin mai ita tafi dadi ni kan baza'aji mutuwa sarki a bakina kawai malama kije yanzu yana "side dinshi ki fallasa masa sirrin zuciyar'ki. Na'eema ta dafe kirjinta da ke barazana tunkudo zuciyarta waje tace " I can't raheela ba zan iya ba ki nemo min wata hanya amma ba da wannan. Mtsss...raheela taja tsoki tace saboda me da bazaki gaya masa ba"? Cikin raunin murya na'eema tace "cos am so scare" Raheela ta tabe tace wannan "scared" din shine zai yi miki katanga karfe da yaa Amar ki dage kiyi fito na fito da shi ki yake shi, yabarki ki kai ga masoyinki. Na'eema tace yanzu mecece mafita"? Raheela tayi shiru kamar mai tunani daga bisani tace mafita guda daya ce...... 🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~2⃣2⃣~ Mafita guda daya ce ina zuwa raheela ta mike tsaye ta nufi wurin "fridge" ta bude ta dauko "jug" mai dauke da fura ta mikawa na'eema tace kafin kaka tafita tace na, kaiwa yaa amar fura don haka kije ki kai masa kuma karki kuskure kidawo batare da kin furta masa kalma so" na'eema ta karbi "jug" din fura ciki'n sanyi jiki ta juya har tayi tako biyu zuwa uku taji murya raheela na kirata taja tayi tsaye raheela tace "oll d best" batare da na'eema tace komai ba tajuya raheela nagani tafita tasauke ajiyar zuciya, sai kuma ta tsince kan'ta cikin yanayi na faduwa gaba dafe kirji'nta tafara furta "innalillahi wa'inna illaihi raji'um"! Kaitsaye na'eema ta doshi dakin amar gaban'ta na dukan tara-tara har ta rike "handling ta bude kofa sai taji sauti muryoyin, mutane sai kawai tafasa budewa a zuciyar'ta tace yaa amar bashi kadai bane to ya zanyi da sakon da ke cikin zuciya taa"? Kamar daga sama taji murya wani daga cikin falon yace haba amar "how long" za ka dauka kana cigaba da "hiding feelings" dinka akan raheela"? Ras-ras-ras sautin da kafita daga kirjin na'eema kenan ta durkushe kasa tasaki kuka mai tsuma zuciya, murya amar taji yana cewa uhmm...kb kenan karka damu ko na furtawa raheela kalma so ko ban furta ba "she is mine & no body can't snatch her from me" Na'eema ta toshe bakin'ta da tafin hannuta don kada su ji sautin kuka'nta. Mtsww....kb yaja tsoki yace wallahi ina tausayawa wannan abari yahuce naka saboda na tabbata shi ke kawo rabon wani, amar ya galla masa harara hade da cewa raheela tawa ce ni kadai matukar ina raye babu wani mahaluki da ya esa ya hau karaga'r mulki zuciyar'ta sai ni Amar matawalle saboda ni nafi cancanta da na mulke zuciyar'ta da gangar jikin'ta yana karasa zance'sa ya fisge sigari da ke hannu kb yayi mata kyakyawar zuqa kb ya zaro ido yace amar kaida ka ke mini fada Shan sigari yau kaine da sha"? Amar ya yatsine fuska yace dole ce takama. Na'eema ta mike da kyar jiri na kwasar'ta da gudu ta nufi "side" dinsu tafada falon umma hajara tana kuka a firgice umma ta mike tsaye tace ke lafiya me ki ke yiwa kuka"? Batare da Na'eema tabawa umma amsar tambayarta ba takara kwasawa da gudu tayi ciki'n "bedroom din umma cikin yanayi na tashin hankali umma hajara ta mara mata baya kwance tarar'da na'eema bisa gado tana kuka tamkar ranta zai fita umma takarasa wurin ta tadagota cikin rawar murya umma tace lafiya na'eema me ki ke yiwa kuka"? Da kyar na'eema ta iya bude bakin'ta tace umma narasa farin ciki'na shikenan umma, narasa yaa amar rashi na har abada cikin rashin fahimta inda ta dosa umma tace bangane abinda ki ke nufi ba na'eema"? Na'eema tace umma yaa amar ashe basona yakeyi ba raheela ce zabin zuciyarsa ki taimake ni umma kar narasa shi,domin rashin shi agareni ba karamar masifa zai sanya ni a ciki wallahi za ki iya rasani..... 🖊excellent writer's🖊 Jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:33 am] Jeeddah Aliyu🌹: ￿￿￿￿🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆￿ ￿💕love story 2016💕￿ Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~￿2⃣3⃣￿~ Umma hajara tadaka mata tsawa hade da cewa ke banaso shashanci banza da wofi yanzu ki rasa wanda zaki, kwalafa ranki akan'shi sai jini'n buzaye jinin da duk duniya na fi tsana to inda ma mafalki ki keyi ki falka saboda bazata sabu ba wai bindiga a ruwa, Ko kin manta da alqawali da nayiwa suraj dan gidan anty asabe na bashi ke"? Na'eema takara fashewa da kuka tace wallahi umma banaso yaya suraj asalima na tsane shi, tsana mai tsananin gaske, umma taja tsoki tace lallai za'ayi bala'e a gidanan don bazan taba amincewa ki aure Amar saboda mahaifiyar'sa itace tushe rusa mini farin ciki'na don haka bazaki aure dan'ta ba kuma karki kuskura nakara jin kin furta kalmar "SO akan Amar sai na zube miki hakora, umma nakarasa zanceta taja dogon tsoki tafice daga dakin, yayida na'eema tacigaba da shashekar kuka'nta. Amar da kb suna fitowa sukaci karo da "jug" din fura ajiye a bakin kofa rass...gaban amar yafadi yadafe kirji cikin yanayi na wanda yashiga firgici yaci na shiga uku, kb kalli nan yanunawa kb "jug" da hannu'shi kb ya tabe baki yace wannan ae jug" ne, Amar yasauke ajiyar zuciya daga bisani yace shikenan raheela tagama sanin sirrin zuciya ta shine ta ajiye min fura anan, cikin tsananin Jin dadi kb yace "Alhamdulillah" abinda nake mafalki yafaru shine yau yafaru, kaga malam ka kwatarda hankali'nka Allah ne yakawo maka sauki kawai yanzu ka je ka kara siye zuciya'rta da zazzafa kalaman soyayya, masu ratsa jinin jiki" ka rikita mata "brain" abokina ta hanyar dada' kalamanka amar ya kyalkyale da dariya yace kai kb bakada kyau an gaya maka ni irinka ne da zan je gaban mace ina zuba ko mace ma karamar yarinya irin raheela ae sai ta rena ni, mtsss...kb yaja tsoki yace chan ta matsi maka watakila wannan girman kai naka shine sanadi da za ka rasa raheela, har amar yayi yunkuri yabawa kb amsa kb yadakatar'da shi ta hanyar cewa sai da safe amar sauri nakeyi na bar madam ita kadai yafada ciki'n motar'sa yaja yafice daga gidan. Amar yayi yana tunani mafita tabbas abinda kb yafada gaskiya ne yakamata nakara jadadawa raheela son" da nakeyi mata saboda boyo da nakeyi mata a yanzu bashida amfani, ya kalli agogo da ke daure a hannu'shi kirar "Rolex" yaga karfe 10:30pm tayi yaja dan karami'n tsoki saboda yasan a irin wannan lokacin kaka ta rufe kofar'ta ba yanda ya iya dole yadauki "jug" din fura shi yashige falonshi zuciyarsa cike da son da kaunar raheela. A WASHE GARI******** Raheela na kwance a falon kaka tana tunani dalilin da yasa na'eema bata kwana a "side" din kaka ba Amar yayi sallama yashigo hannusa dauke da "jug" fuskar raheela dauke da murmushi ta amsa hade da cewa ina kwana yaa Amar"? Amar ya murtuke fuska sai kace tsohon soja yaja birki a bakin kofar shigowa yace ke zo nan ciki'n sanyi jiki raheela ta mike ta nufi wurinsa gaban'ta sai faduwa yakeyi a zuciyar amar yace kai kaga yarinya tun ma kafin na furta kalma SO" a gaban'ta tafara rena ni mtssss....shine matsala soyayya da kanana yara raheela ce ta katsi masa zance zuci sa ta hanyar cewa yaa Amar gani. Kallon uku saura kwabo yayi mata daga bisani yace uban me ki ke yiwa dariya"? Gani yadda ya murtuke fuska, yabawa raheela dariya batasan lokacin da ta kwashe da dariya ba amar yakara harzuka yadaka mata tsawa yace abin ki iskanci ne koh Raheela"? Da sauri ta hadiye dariya'rta ta hanyar toshe bakinta da tafin hannuta" Amar yacigaba da cewa don tsabar iskanci shine jiya kika yi min labe ki kaji abinda nake fada bayan kingama mini labe a maimakon ki shiga ki kai min fura ta sai ki ka ajiye a bakin kofa koh"? Raheela ta zaro manya idanuta hade da girgiza kai tace yaa Amar b...... yadaka mata tsawa shiru banaso jin komai daga bakin'ki yakara matsowa daf da ita har sunaji bugun zuciya'r junan'su yayi kasa da murya yace duk abinda ki kaji a dare jiya a dakina gaskiya ne raheela babu karya a ciki, yakarasa magana hade da daga mata gira, raheela ta turo baki tace nifa yaa Amar ba abunda naji ehee" Ya galla mata harara yace karya ki keyi munafuka in bakiji firar da mukeyi ni da kb miyasa ki ka kasa shiga ki kai mun fura sai ki ajiye a bakin kofa"? Raheela ta murguda baki tace haka kawai" Amar yace haka kawai ki ka ce"? Raheela ta zaburo baki tace eh" haka kawai, amar yayi murmushi mugunta yace "good" ya bude murfi "jug" din ya juye mata ragowar fura da ke ciki'n a jikin'ta yakara tanke fuska yace na baki na baki "ten minutes" kije kiyi wanka ki samini a "parking space" zan daura miki karatu daga inda ki ka tsaya da jin firar mu ta jiya ya kuma saka dan yatsa sa ya lakato fura da ke bisa kumatu ta ya lashe yace "just ten minutes" yajuya yafice daga falon raheela tafashe da kuka gashi kaka batanan ballatana ta tare mata wannan wulakanci'n na amar haka ta juya tashiga "bathroom" tana kuka. Wanka takeyi amma tana tunani wace irin fira ce yaa Amar sukeyi da na'eema tayi labe tanaji"? To ko shine dalilin da yasanya yaya na'eema bata kwana a side nan ba"? Cab ae kuwa dole yaa Amar ya saurare ni na wanke kaina ta hanyar fada masa bani bace da wadanan tunane-tunane raheela ta gama wanka ta dauro "towel batare da tayi "make up" ba tasaka riga da siket na "blue lace mai touch din pink tafasa turare "pink heart" ta yane kanta da dan karami'n "veils shima pink duk da batayi "make up" ba tayi matukar kyau na ban mamaki har ta juya za ta fice daga dakin karaf idanu'ta suka sauka bisa "side bed drawer" ta bude tadauki "lollipop" dinta guda daya ta bare ta jefa ciki'n baki tana tafiya tana tunani yadda za ta wanke kanta wurin yaa Amar...... ￿￿🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆🍆￿￿ ￿💕love story 2016💕 Na Hauwa shehu Aliyu🌹 ~￿2⃣4⃣￿~ Amar da ke zaune bisa boot" din mota ya tsurawa raheela idanu tsananin sonta na kara samu muhali a zuciyar'sa ya lumshe idanu shi. raheela tacigaba da zance zuci ta hanyar cewa na shiga uku yaya na'eema kin daza min masifa kalli yadda "guy" nan yasha "omo ba shakka yau sai naci dan kare duka a wurinsa. Raheela na karasawa "parking space" daga nesa da shi taja tayi tsaye, amar yayi mata wani mugun kallo wanda yayi sanadiyar da hanji cikin'ta ya murda da Sauri takarasa gabanshi tsura mata idanu yayi yana mata shu'umin kallo wanda yasanya raheela shiga ciki'n bakon yanayi wani rikitace sanyi ya ratsa kassa jikinta tamkar sanyi hunturu yayida tsigar jikin'ta ta, tashi zuciyata na bugawa da sauri-sauri Amar yasaki murmushi samu nassara saboda yasan 'yar karamar kwakwalwa raheela tadauki sakon da ya tura mata, tuni jikin raheela ya mutu takasa sarafa kan'ta" Amar yacire "lollipop" din bakin'ta yajefa a nasa baki yana tsotsa yabar raheela sake da baki tana masa kallon kana rikita ni fa suna hada ido yakashe mata ido hade da cewa yadai da sauri ta sunkuyarda kan'ta kasa Amar ya kira sunanta Chan kasan makoshi, da kyar ta kalli shi, gani har yanzu "sexy eye's" dinsa suna kafe akan fuskar'ta yasa ta murguda masa baki tare da cewa yaa Amarrr...yadda ta kira sunan shi yasa Amar yaji yarrrr....yana yawo a gangar jikinsa nan take yakara jin wani sabon sonta yana kwarara a zuciyar'sa kamar daga sama yaji muryar raheela cikin shagwaba tana cewa ni daina yi min wannan kallon naka na "magic" Amar ya dan murmusa tare da cewa yau kuma nan ki ka koma"? kin gama kira na da mai idanu "horror" raheela ta turo baki tace to ae gaskiya na fada kuma sai na fadawa kaka wulakanci da kayi min. Amar ya tabe baki yace ke fa bakyaso, a zauna lafiya yaushe nayi miki wulakanci"? Raheela tace wanke ni da fura dakayi batare da nayi, maka laifi komai ba" Amar yayi murmushi'n yace mari naso na wanke ki da shi sai ki ka ci sa'a "jug din fura yana hannu na da in na wanke ki da Mari sai hakora ki sun fita, raheela ta zaro idanu tace cab mari fa"? Ya galla mata harara tare da cewa ko kin wuce mari ne"? Raheela tayi fari da idanu tace "Nop" ko duka na za ka iya Amar yace miyasa jiya ki kayi min labe"? Raheela tace ni fa daina cewa nayi maka labe, Amar yayi murmushi'n tare da cewa nadaina yaya raheela" jin suna da ya kirata da shi, yasa ta kyalkyale da dariya tace ka rufa min asiri yaa Amar wannan sunan yafi karfin shekaru na, Amar ya shafi sumar kanshi yace raheela kinsan me SO yake nufi"? Raheela tayi murmushin tace wannan Wace irin tambaya ce yaa Amar"? Amar ya hade fuska yace na tsani nayi tambaya a mayar mun da tambaya a maimakon amsa "so take note" raheela tayi shiru tana kallon'shi ya zaro idanu yace ki bani amsa mana raheela ta rausayarda kai tamkar za tayi kuka, tace yaa Amar "SO" sai kuma tayi shiru kamar mai nazari gani haka yasa Amar yace kince SO kiyi shiru ko kina nazari ne"? Cike da shagwaba raheela tace, "SO wata halinta ce da ke shiga jikin dan-adam batare da sani sa ba '"SO baya neman izzini a lokacin da zai sami muhalli a zuciyar dan-adam cuta ta SO batada magani illah samu amincewa zuciya'r da ka ke SO" tun lokacin da tafara magana Amar yake kallon dan karami'n bakin'ta mai dauke da "pink lips" tana dasa aya a zanceta Amar yadauki tafi raf-raf-raf yaciro lollipop" din da yake tsotsa yasaka mata a baki dai-dai lokaci'n da na'eema tafito a "compound" din gidan karaf idanu'ta suka hasko mata amar yana sanyawa raheela "lollipop" a baki runtsa idanuta tayi hawaye na zuba akan fuskar'ta amar yace baby sha lollipop" kafin nayo miki "special shopping" saboda kin gama tafiya da zuciyata raheela ta kyakyace da dariya, amar yace dole kiyi dariya "baby domin kin sanyaya zuciyar da ke muradin ki kafin nayi miki fashi'n baqi fada mun inda ki ka samu wadanan zazzafa kalamai"? Raheela ta turo baki tace a hausa Novels" Amar ya zaro idanu hade da cewa eh" lallai kam yarinya kinyi nisa ni ina nan ina miki kallon karamar yarinya ashe kin wuce da sani na maganar kb ta tabbata mudi'n na tsaya wasa zan rasa ki, jikin raheela yayi sanyi sakamako jin kalamai amar masu halshen damo, Amar yayi gyaran murya ya murtuke fuska yace raheela ki natsu ki bude kunne ki da kyau yau zan baiyana miki sirri'n zuciyata, tuni jikin'ta yafara jikewa da gumi zuciyar'ta tashiga wasiwasi me yaa Amar yake nufi, yayida Amar yacigaba da cewa tun ranar'da ki ka zo duniya banida wani mafalki da ya wuce naki raheela, zuciyar'ta ta kamo da tsananin son'ki tun lokacin da bakisan miye duniya ba wani irin yanayi raheela tashiga mai wuyar fassarawa nan take ta nemi natsuwa'rta tarasa hakan ne yabawa Amar damar Cigaba da tona asirin zuciya'rsa, ke ce farin ciki'na raheela gaba daya rayuwa ta na tsara ta ne tare da ke, bantaba kallon wata 'ya mace da sunan SO sai akanki raheela, kuma bana bukatar jin amsa kin amince ko baki amince ba daga bakin'ki saboda zuciyata ta tabbatar min da kema kina sona, don haka kifara shirye-shirye biki saboda aure nakeso nan da dan kankani lokacin inaso afara kirana da "daddy yakarasa magana hade da daga mata gira. Raheela tasauke katuwar ajiyar zuciya ta kuma share gumi'n da ke fuskar'ta da mayafinta, tayi zurun tana kallon Amar zuciyar'ta tamkar zata fado kasa don tsanani tsoro da rudani da tashiga wai ita yaa Amar yakeso anya kuwa Wannan lamari na yaa Amar akwai kamshin gaskiya a cikin'sa"? Mutumi da yafi kowa tsanata yau shine tsaye a gabana yana furta mini kalma'r SO" in har da gaske ne yaa Amar yana sona to yaya na'eema fa"? Kai ba zai yu ba ni ba sakarai bace da zan amince da makiyina a matsayin masoyina kuma ba zan iya taba cin amanar 'yar Uwa taa gani shiru nata yafara yawa yasa Amar ya kira sunanta Chan kasan makoshi'nsa raheela wani irin "shock" taji amma sai tadake tayi wani dagowa tana masa kallon sama da kasa tana yatsinar fuska daga bisani ta kyakyace da dariya tace...... 🖊excellent writer's🖊 Jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:33 am] Jeeddah Aliyu🌹: ￿￿🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆￿ ￿💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~￿2⃣5⃣￿~ Tace lallai yaa Amar ka haukace, kai yanzu don bakada kunya za ka dubi tsabar ido na kace kana sona ae ni ko maza suka kare a duniya ba abinda zanyi da kai, kalle ka fa wani jingege da kai, in kamanta yaa Amar na tuna maka ka sha fada mini cewa ka tsaneni bakaso na don tsabar kwarewa da iya yadaura da son bata zumuncin shine za kace kana sona to ni banaso'nka kuma na tsane ka, tun lokacin da tafara wankewa Amar allo'nsa yake kallon'ta batare da yayi yunkuri katsita ba saida tagaji don kan'ta tayi Shiru tana sauke numfashi'n Amar yadiro daga sama "boot" din mota fuskar sa tayi jajir don tsabar fushin ciki'n zafin nama yadanko hannu raheela ya dago habarta da hannu sa guda, ya tsura mata idanu, ciki'n sarkewa halshe raheela tace miye haka yaa Amar? wannan ae hauka ne kasake ni karka ji min ciwo Amar yakara zaro idanu yace duk duniya ba abunda na tsana irin rashin kunya, don nace ina son'ki bashi zai baki dama ki renani ba ni mutum ne mai matukar son girma, kinga kuwa dole ki girmama ni kuma dole ki soni, ke ba ma abin alfahari ne a wurin'ki a matsayin, da nakeda shi na bude baki nace ina so'nki "who do u think u are"? Ya sauke gwaron numfashi yasake habarta ya matsi "lips" dinta batare da yajira jin ta bakin raheela ba yacigaba da zazzaga mata masifa mai cike da gargadi, in har kina tunani yaudara ki zanyi kinyi kuskure raheela saboda tun kafin wadanan "ball's" din sunfara fitowa a kirji'nki nakeso'nki yanuna kirji'nta da yatsan shi, in kuma kina tunani don kyau ki nakeso'nki shima kin tafka kato kuskure saboda, akwai mata da yawa suka fiki kyau da a duniya, iya abu daya nasani raheela son'ki ina miki son da bana yiwa kaina shi ni mahaukaci ne akan son'ki don haka ina mai baki umarni ki bini a hankali domin ni mutum ne mai wuyar sha'ani zan iya ajiye son da nakeyi miki a gefe nayi miki dukan tsiya in yaso daga baya na rarrashe ki da zazzafa'r soyayya ta wannan shine salo naa sai ki kiyaye yana karasa zance'sa ya ture ta tayi tangal-tangal za ta fadi ya riko hannuta yajanyo ta da karfi saura kiriss....tafada kirjinsa sai kuma ta tsaya da kafafu'ta yasoma yi mata rikitace kallo mai cike da so da kauna na'eema da ke jingine jikin fila tayi zurun tana kallon su idanu ta na zubar'da hawaye masu masifar zafi, amar yasa hannu yarike tsinke "lollipop" din da ke bakin raheela yafisgo shi da karfi, yayida hawaye suka wankewa raheela fuska tarasa wane irin cin zarafi za ta yiwa Amar domin ta huce takaici wannan bakin ciki da yaguma mata bata ankara ba taji ya murda mata hannu runtsa idanuta tayi saida yakara mata kallon wulakanci yasake ta daga bisani yanuna mata hanya da yatsa yace oya shiga gida, ki je kiyi jinyar zuciya da gangar jikin'ki ni zan fita in nadawo zan daura miki daga inda muka tsaya kinsan ni soyayya taa mai zafi ce bana gajiya da aika sako'ni, raheela ta share hawaye da bayan hannu'ta jin takeyi kamar ta shako wuyan Amar tayi ta duka'nsa har sai masu gadi Sun kawo masa dauki saidai ina ba abunda zai yuwa bane sata lahira akawo duniya wannan shi ake kira fin karfi, gani tayi shiru sai hawaye ke zuba akan fuskar'ta yasa yadaka mata tsawa ciki'n hargowa yace dallah malama wuce ki shiga gida kinyi wani tsaye kina hawaye munafuci salon wani yaganki ace nafara cutar'ki tun kafin a daura mana aure da gudu raheela ta juya tanufi ciki'n gida na'eema nagani haka itama ta falla da gudu, Amar yabi bayan ta da kallo a baiyane yace ina son'ki baby naa" yajuya ciki'n nishadi yashiga motar'sa yaja yafice daga gidan kaitsaye ta shige "bedroom din kaka tafada bisa gado tafashe da kuka tace "I hate u yaa Amar wallahi na tsane ka ba yanda za'ayi na so ka haka kawai ina zaune lafiya da 'yar uwa taa kanaso ka haddasa gaba a tsakani mu yanzu me zai faru in yaya na'eema taji yaa Amar ni yakeso ba ita ba"? Wani bangare na zuciyar'ta yace ke ma raheela shashasha ce ya za'ayi Amar ya so ki shin ko kin manta tun kina yarinya yaa Amar bayaso yaganki cikin farin ciki"? Yayi amfani da kalma SO" ne kawai don yasanya ki cikin 'kuncin na'eema ita ce tafi dacewa da shi domin ita yake nunawa SO sabani ke da yake nunawa baiyananiya kiyayya, lallai yaa amar dan reni "senses" ne na bugawa a jarida, amma zan nuna masa cewa kan magge yawaye...... 🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~2⃣6⃣~ Raheela tacigaba da zance zuci gani haka ba Zai fishe ta ba yasa ta share hawaye ta, bacci yayi awo gaba da ita. Da gudu na'eema tashiga falon tafada jikin umma hajara tafashe da kuka umma tace oh ni hajara ina zan saka kaina da wannan masifa da takunno kai a gida na to kuma yanzu me faru ki ka shigo min falon da gudu kina kuka"? Na'eema takara fashewa da wani sabon kuka tare da cewa ki dubi girma'n Allah umma ki ceto rayuwata daga afkawa halaka umma ni kadai ki ka haifa in na mutu bakida wasu 'ya'ya da za ki kalla a matsayin ke, ki ka haifa ki taimake ni umma kar narasa yaa amar wallahi umma ina sonshi ina yi masa mahaukaci SO da zuciyarta, bata iya jure ganisa da raheela umma in har narasa yaa Amar nima za ki rasa ni domin zan sha ''poison" na kashe kaina a firgice umma hajara tadago na'eema, ta wanka mata mari tace kan'ki daya na'eema da zaki kashe kan'ki akan wani banza" to ki kwatarda hankalinki domin ni uwa ce mai son farin ciki 'yarta koda ace zan dawo yawo tsirara a gari sai na kwanto miki soyayya'r amar kuma nayi alqawali sai na tarwatsa rayuwar raheela tun tayi sanadi zubar hawaye ki yadda ki kayi kuka akan Amar ita ma sai tayi kuka akansa so nake ciwo zuciya yazamo shine, ajali'nta don haka maza share hawaye ki ciki'n tsanani jin dadi na'eema ta share hawaye tace umma yanzu ya za'ayi saboda banaso na bude idanu na nagansu tare"? Umma hajara tayi dariya mugunta tace sha kurumin'ki na'eematu boka duguzuu shine mai magani 'ya'ya iska na'eema tayi murmushi tace da kyau umma so nakeyi raheela tagano cewa tayi babba kuskure naso abunda nakeso tagano cewa ba'a tabani a kwana lafiya Umma tace to ki bude kunne ki da kyau ki saurare huduba da zanyi miki na'eema ta gyara zama tace na bude umma wani kafiri murmushi umma tayi daga bisani tace daga yau karki kuskura ki kara shiga "side" din fateema ki kuma tataro duk wani abu da ya kasance mallaki ne ki baro bangare kaaka kidawo nan da zama inaso ki daura gaba da mutane gidanan domin ba kauna sukeyi ba kuma banaso ki kara kowace irin hulda da raheela tsakani ki da ita kiyayya ce mai zafi, na'eema tace angama umma hudubar ki ta zauna a kwakwalwa ta saboda yanzu babu saura kaunar raheela a zuciyata asalima jin nakeyi kamar na daba mata wuka a kaho zuciya umma hajara tayi murmushi jin dadi tace tashi maza ki je ki tataro kayanki na'eema ta yatsine fuska tace tun yanzu umma? Eh mana ae ba'a bori da sanyi jiki na'eema ta mike tanufi "side"din kaka.... Jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:33 am] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~2⃣7⃣~ Kaitsaye na'eema tashiga falon kaka, gani babu kowa a ciki yasa ta wuce "bedroom" din kaka taya tayi tsaye sakamako, hango raheela kwance tana bacci taja tsoki mtsss...a baiyane tafara magana banza munafuka maciyiya amana raheela da ke ta shara baccin ta bata masan tana yi ba na'eema jin takeyi kamar tashake raheela ta mutu kowa ya huta,cikin zafin rai ta bude "wardrobe" da karfi tasoma kwaso abinda yake mallaki ta, ta jingewa kasa, yanayi ta tamkar na mai tabin hankali karar budewar "wardrobe" ne yayi sanadiyar falkawa raheela, cikin tsananin mamaki ta ke kallon na'eema, da ta iya bude bakin'ta dalilin nauyi da yayi mata ga kuma wani masifafe ciwo kai da ke barazana, tsaga mata kai tace lafiya yaya na'eema ki ke kwashe kayanki"? Banza tayi da ita tamkar bataji tambaya da tayi mata ba tadauko katuwar "trolley" dinta tasoma dibar kayan da ta jinge kasa tana zubawa ciki'n "trolley" da sauri raheela tasauko bisa gado ta riko hannu na'eema fuskar'ta dauke da tsantsan damuwa, tace dan Allah yaya na'eema kiyi min magana me ke faruwa ne"? Ciki'n bacin rai na'eema ta buge mata hannu tadaka mata tsawa cikin tsabar masifa da bala'e tace dallah ki saurara min haka nan ko kina tsanmani banida masaniya dangane da zago kasa'n da ki ke yi min"? Cikin rashin fahimta inda zance'ta yadosa raheela tace ni fa yaya na'eema kina kara jefani ciki'n rudani saboda ban fahimce manufar wannan zance naki mai kama da halshen damo ba, na'eema taja tsoki kamar za ta gutsiri halshen'ta hade da cewa kada Allah yasa ki fahimta abu daya nakeso kisani raheela banza irinki bata esa tarabani da Yaa Amar domin abin abaiyane yake duk fadin matawalle family ba wanda baida masaniya ni yaa Amar yakeso ba ke inda ma wani kulle-kulle ku ka kulla ke da munafukar uwar'ki to ta Allah bataku ba, domin ni da yaa Amar mutu karaba ne takalmin kaza nan gani nan bari dukiyar uban wani tana karasa zanceta taja "trolley" din'ta da karfi tafice daga daki'n yayida tabar raheela tsaye ciki'n wani hali, hawaye na zuba akan fuskar'ta, ta durkushe a tsakiyar daki takara fashewa da sabon kuka kamar wanda aka aikowa da sakon mutuwa, tasoma sabbatu, buri ka yacika yaa Amar shikenan karabani da 'YAR UWA TAA" ka hadasa gaba a tsakani mu me nayi maka yaa Amar da ka zabi wannan hanyar don ka musgunawa rayuwata"? Jin andafa kafada ta yasa tajuya gani kaka tayi tsaye fuskar'ta dauke da damuwa da sauri ta mike tsaye tafada jikin kaka tasaki kuka mai tsuma zuciya mai karatu, ciki'n sigar rarrashi kaka take bubuga bayan'ta da kyar kaka ta rarrashe ta tadaina kuka, kaka ta zaunar'da ita a gefe gado tasoma tambaya'r ta dalilin kuka'nta raheela ta kwashe iya abunda tasani tafadawa kaka kowane su yayi shiru sai kace masu nazari daga bisani kaka tayi murmushin takaici, hade da cewa babu zance yaudara a ciki'n zance da amar yafada miki da gaske ne yana sonki raheela saidai ni kaina ina mamaki wannan halaya ta Amar iya abunda nasani kowane dan-Adam yana kokari yaga ya kyautatawa abinda yakeso sabani amar da yake munanawa abinda yakeso yana farantawa abinda bayaso rai tabbas raheela" amar yana son'ki so da shi kan'shi ba zai iya misalta shi, ba a tsorace raheela tace haba kaka miyasa wannan karo ki keso ki goyi bayan yaa amar"? duk fadin gidanan ba wanda baisan yaa amar ya tsaneni baya sona wannan al'amari a baiyane yake kaka. Kaka tace ba tsanarki yakeyi ba raheela son'ki ya ke yi wallahi amar yana tsanani son'ki soyayya'r da amar yake miki tasamo asalin tun daga ranar da ki kazo duniya ni shadace akan haka, ki yarda da ni raheela kinsan bantaba fada miki karya ba kuma kinsan ina adawa da duk wani abu da yayi yunkuri shiga tsakani ki da farin ciki ki, amma azahari gaske inaso ki da amar domin amar yar.o ne nagari kuma kowace uwa tanaso 'yarta ta aure miji nagari shiyasa nake miki sha'awa kasancewa da amar. Raheela ta turo baki tace wallahi kaka banaso shi na tsaneni shi don haka kifada masa ya kyale ni yaje ya rungume me sonshi, kaka tayi zugun tana kallon raheela daga bisani tace dama abinda nake yiwa amar gudun kenan tsuntsu da yaja ruwa shi ruwa kan doka wannan shiri sa ne shi, kuma yasan yadda zai gyara kayansa. Raheela ta tabe baki hade da miqewa tsaye tace dan Allah kaka kije kidawo da na'eema ki kuma fada mata cewa ni banaso yaa amar shi kadai ne yake shirme sa. Kaka ta galla mata harara tare da cewa ae bani nakori ta ba da zanje nadawo da ita, raheela tayi kasa da murya tace dan Allah za kije ba don halina ba kaka taja tsoki mtsss....ta mike tafita tabar ma raheela daki... 🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~2⃣8⃣~ Raheela ta mara mata baya sai faman yi mata magiya takeyi ciki'n fushi kaka tace wai ke wace irin maya yarinya ce"? Wannan rashin zuciya naki yayi yawa, to ba inda zan je don ni ba shashasha bace irin'ki in har ke damu da rashin ta sai ki tatara komaitsa ki, ki koma bangare su da zama. Raheela ta bata fuska tace Shikenan kaka ki sha zaman ki yaa amar dai ne nace banaso shi duk mai daukar zafi da ni yayitayi ni ko a jikina, tana karasa zanceta batare da tajira jin ta bakin kaka ba taficewar'ta. "side" din mamee tanufa a falo tarar'da mamee zaune tana kallon tashar sunnah tv raheela tayi sallama mamee ta amsa mata "direct" ta zauna kusa da mamee ta dan kwato da jikinta a jikin mamee tace wash....Allah na nagaji mamee ta tabe baki tace, da ki kayi aiki me"? Raheela ta Yatsine fuska tace aiyuka da yawa mamee ta ture tace ke dagani banaso shiririta duk wanda aure ki yana da aiki, ciki'n shagwaba raheela tace nifa mamee danki zan aura. mamee tayi dariya hade da cewa dadi na da ke raheela rashin kunya mu ae ba mahaukata bane da za mu hada ki aure nazeer, raheela ta tunzire baki tace wai saboda me"? Mamee tace saboda daga ke har shin din bakuda ta natsu raheela ta tintsire da dariya tace kai mamee yanzu kallon motsatsu ki keyi mana"? Mamee tace kwarai kuwa" raheela takara tintsirewa da dariya har tana fadawa jikin mamee, sallama amar ce takatsiwa raheela dariya da takeyi ta wani bata fuska shima batare da ya kalle ta ba ya kai zaune, mamee tace kawo maka abinci ne"? Amar ya shafi sumar kan'shi wanda ya zame mishi dabi'a daga bisani yace banaji yunwa a koshe nake. Raheela ta mike tsaye tace mamee na tafi sai anjima, zan dawo nayi miki gyara "wardrobe" mamee taja tsoki tace nasan halin ki raheela ni da kara ganinki sai kuma gobe ko don kin fahimci nafiso naki da na na'eema, ne shiyasa ki ke mini yawo da hankali raheela tayi dariya tace Allah mamee zan dawo mamee tace adawo lafiya raheela tafice daga falon, amar da ke lumshe da idanu kamar mai bacci ya bude idanu shi, shima ya mike tsaye hade da cewa mamee inaso kiyi min dambu nama in tafi da shi, mamee ta tabe baki tace yakamata kayiwa kan'ka fada ka ajiye iyali haka nan amar dan murmusa batare da yace da mamee komai ba yafice, raheela na fita daga falon mamee tanufi "garden" ta nemi kasan "grass carpet" ta zauna har cikin zuciya'ta tanaso taje tabawa na'eema hankuri ta kuma fada mata ita bataso'n yaa amar saidai tanaji tsoro masifar umma hajara domin kuwa tono silili Za tayi mata wanda janyo kowa yagama Jin amar yace yana sonta kuma hakan zai iya kara haifar da gagarumar matsala mtss....taja tsoki yaa amar yacuce ni, ya jefani cikin damuwa ina zaman, zama na ciki'n kwanciyar hankali ni da 'YAR UWA TAA gashi ya haddasa mana gaba ko me zai faru in na'eema tafadawa umma hajara ni yaa amar yakeso ba ita ba. Gaskiya yaa amar mugu ne duk wa shekaru nan yasan ni yakeso miyasa yake nuna min zallah kiyayya yake kuma nunawa na'eema tsantsan so"? Tun lokacin da raheela tafada kogin tunani amar yake tsaye a bayan'ta gani ta tsunduma da yawa yasa ya karyo ganye bishiya mangwaro ya aza mata bisa wuya, a firgice ta mike tsaye tana kurma ihu Amar ya kyakyace da dariya daga bisani ya tsagaita da dariya da yakeyi yace ya akayi ne "baby naa" wannan ihu duk na menene"? Kallon tsana raheela tafara aika masa daga bisani ta ja wani wawa tsoki tajuya da suna tafita daga "garden" din ciki'n zafin nama yariko hannuta... Jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:34 am] Jeeddah Aliyu🌹: [6:13PM, 5/8/2016] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~2⃣9⃣~ Batare da tajuyo ba tace dallah malam kasake min hannu, yayi murmushi yace in kinada karfi ki fisge hannu naki mana, tace kasan bazan iya ba shiyasa ka ke wannan karadi" ya make kafada yace wai me kike nufi da ni ne uhmm"? kina gani na falon mamee ki ka tsare na biyo ki nan kuma kinaso ki kara tsarewa me hakan yake nufi"? Raheela tace dan Allah yaa amar ka kyale ni kafita daga rayuwata iya abunda nasani ba'a soyayya dole, nace banaso bana sonka bana kaunar'ka ka kyale ni mana kaje ka rungume yaya na'eema domin itace take fama da haukan sonka, ka nisanta daga gareni in har baso ka keyi nayi maka, rashin mutuncin. A harzuke yakara matsi hannu'ta yace ki san irin furucin da ki kefada mini domin na fahimci kinaso ki wuce makada da rawa in har akan sonki ne ashirye nake da na shanye duk wani rashin mutuncin ki, dole kafadi haka yaa amar saboda kanaso ka tarwatsa min farin ciki da jin dadi bansaba da damuwa karka kace za ka hadasa mini shiga cikin'ta, in har da gaske tun ina yarinya ka keso na miyasa ka kasa reno zuciyata da sonka"? Batare da ta jira jin ta bakin'sa ba tacigaba da cewa, sai ka zabi hanyar ka cusa mini kiyayya ka ka dinga nunawa yaya na'eema son da kulawa wanda yayi sanadi da ta afka kogin sonka, shine yanzu don bata basira za ka zo kace kana sona to ba zan boye maka ba koda za ka yanka ni bana sonka aslima ka kara daura mini tsanarka a zuciya, domin kana yunkuri, rabani da 'yar uwa ta so ka sake mini hannu tsakanina da kai kiyayya ce mai zafi. Har ta dasa aya a zanceta Amar yana kallon ta yasauke katuwa ajiya zuciya, hade da cewa zance banza zance wofi, ita na'eema wane kare hauka ne ya cije ta da har tayi sake sona yasami muhalli a zuciyar'ta tabbas ta, tafka kuskure mafi muni a rayuwata domin ni ko a kafa aka daura min ita zan kwance na yarr saboda bana sonta ke nakeso raheela ke ce mafalki na, ke ce farin ciki'na ki tausayawa rayuwata ki bani dama zan koya miki yadda za ki soni. Raheela tafashe da kuka cikin shashekar kuka tace wallahi bana sonka yaa amar bana kuma fatar na so ka, kayiwa rayuwata adalchi ka kyale ni karka jefa ni cikin matsala. Tsawon lokacin suka dauka a tsaye ba wanda yakara cewa komai sai sautin kukan raheela, ne ke tashi daga bisani amar yasausauta riko da yayi mata chan kasa makoshi yafara magana ba zan iya rabuwa da ke raheela son'ki yariga yayi min illah, ki taimaki rayuwata ki aura ni zan shayar'da ke tsantsan farin ciki zan wanke duk wata kiyayya da ki keyi min na maye gurbinta da zazzafa soyayya ki yarda da ni "baby naa" ni makaho ne a son'ki. Wani murmushi takaici raheela tayi tace miyasa yaa amar ba za amfani da kwakwalwa ka, ka fahimce cewa matukar yaya na'eema tana raye ka haramta da raheela, a tsorace ya kalle ta jikinsa sai faman rawa yakeyi kamar mazari idanu shi sun kada sunyi jajir, sai huci yakeyi kamar zaki da yakeji yunwa, Ciki'n hargowa yace baki esa ba raheela baki esa ki haramta min kan'ki akan wata banza koda ace narasa ki ba zan taba son na'eema za je na sanarda iyayye mu domin nasan su ba za su hanani ke ba,yana karasa zance'sa yayi wulgi da hannu'ta yajuya har yayi tako biyu zuwa uku raheela ta kwada masa kira ya tsaya chak da gudu takarasa gabanshi ta zube tayi "kneel down" ta daga hannaye ta tasoma roko sa cikin rauni murya, ka dubi girman Allah Yaa Amar karka sanar'da su daddy wannan zance ka bani lokacin zan rarrashi zuciyata ta amince da soyayya'rka. Ya dan murmusa yace wannan shawara ce mai kyau amma a wuri'nki tabbas gobe in har ina numfashi kafin na koma abuja sai na sanar'da su daddy abinda ke tsakanin'mu, wani abu da bakisaniba raheela kaka tana goyon bayan aure na da ke kin ga kenan bakida wani zabi, illah ki karbi tayin soyayya ta. Cikin konar zuciya ta mike tsaye ta ja dogon tsoki tace har abada bazan taba son Mugu mai son datsi igiyar zumuncin irin'ka ba tajuya tashiga gida tabar amar tsaye kamar "lamination" tana shiga falo tafada jikin kaka tasaki kuka dan Allah kaka ki ce yaa amar yarabuda ni banaso shi, in har yayi sanadiyar da su daddy suka tilassa min aura shi sai yayi danasani furta kalma so akai na. Kaka tayi murmushi tace to naji amma wannan koke-koke ya esa haka nan ki share hawaye ki ba zan taba goyon baya ayi miki aure dole ba cikin jin dadi furucin kaka raheela ta share hawaye ta. WASHE GARI******** Amar zaune a falon kaka raheela na gefe zaune ta sunkuyarda kai kasa kamar munafuka, kaka ta ajiye casbaha hannu'ta tace Amar dalilin da yasa nace ka zo ada ban so na shiga wannan al'amari naku ba saboda ba tun yau ba nayi ta yima kukan faruwa hakan da yake kai ba'a chanza maka ra'ayi ga duk abunda kasa gaba to gashi abinda ka janyowa kanka nafi kowa farin Ciki in aura yakasance a tsakani ku amma bana goyon abinda Zai bata zumuncin don haka tunda raheela tace bata sonka ka hakura da ita ka aure na'eema kuma karka kuskure ka sanar'da iyayye ku wannan zance cikin tsananin tashin hankali yadago yana kallon kaka daga bisani ya mike tsaye yace kaka banaso na'eema kuma har abada ba zan taba son ta"raheela ita ce wanda zuciya ta takeso matukar narasa ta saidai na mutu banyi aure ba yana karasa magana yafice daga falon kaka tafara kwala masa kira amar"amar kadawo nace bangama fadar abinda nakeso fada ba ko yajuyowa bai yi ba ballatana kaka tasa rai zai amsa mata kira da takeyi masa, kaitsaye yanufi "bedroom" dinshi yadauki "briefcase" dinsa da keys din mota da na dakinsa yarufe kofar dakin nasa ya wuce "part" din mamee a gaugauce yayi mata sallama, mamee tace lafiya amar irin wannan sauri haka kai da kace sai da yamma za ka koma"? Mamee a "hospital" ake nema na urgently" saboda za mu tafi wata "seminar" da kungiya "who ta shirya a lagos mamee ta washe hakora tace kayi kokari kafin kadawo ka je "company" ka gano mini wannan sarkin shiririta baso zaman sa lagos nakeyi ba alhaji ne kawai ya matsa. Amar yayi murmushin yake yace mamee ae yana tare da su abdul za su bashi kulawa, so kidaina damu kanki, ni zan tafi "mamee tace Allah ya tsare ya kai ka lafiya bada mugun gudu, amar yayi murmushi hade da cewa "ameen yafice a "compound" din gidan yaci karo da Lantana mai aiki'n mamee ta runsuna ta gaida shi tace likita ba dai tafiya za kayi ba gashi ba'a kamalla maka dambu nama ka ba"? Sauri nakeyi lantana sai in nadawo next week"sai ayi min wani mu je wurin mota na baki sako ki kai ma raheela...... [8:59PM, 5/8/2016] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~3⃣0⃣~ Ya bude mota yadauko biro da takarda yayi rubutu akai ya miqawa lantana yace gashi ki kai mata amma karki bari kaka tagani, lantana ta karbi takarda daga hannu'shi, tace Allah ya tsare hanya yace ameen ya shiga mota yaja yafice lantana tajuya tashiga "part" din kaka raheela da kaka na zaune inda amar yabarsu tashiga da sallama kaka ta amsa mata, ta nemi wuri ta zauna raheela tace ke kuma daga ina naga kina wani misimisi da baki sai kace munafuka"? Lantana tayi murmushin tace mamee ce ta aiko ni wuri'nki tace tana kiranki raheela ta zaro idanu hade da cewa lafiya take nema na? Yoo ni ina zan sani kawai tace mu zo tare, raheela ta bata fuska tace naji sai ki tashi mu tafi suka mike tsaye a lokacin daya suka fita daga falon. "PART DIN UMMA HAJARA********** A part din umma hajara kuma na'eema da umma sun gama shiri su na zuwa, waje boka duguzuu na'eema tadauki "handbag" dinta tace umma dan Allah kiyi sauri banaso yaa Amar ya koma abuja batare da ya furta mini kalma so, umma taja tsoki tace ke ni banaso gaugawa domin aikin shedan ce, na'eema ta turo baki da misali karfe 11:15pm suka dauki hanyar kauye da boka duguzuu yake sai misali karfe 2:09 na rana suka esa na'eema sai korafi nisa wurin takeyi inda suka saba "parking duk lokacin da suka kawowa boka duguzuu ziyara ana na'eema tayi parking" su karasa da kafa tun kafin su shiga bukka boka duguzuu umma hajara ta fadawa na'eema sharuda boka, da yake yau sun tarar'da layi saida sukayi jira na tsawon mintuna 30 babu zance sallah azahar daga bisani layi yazo kansu suka shiga boka duguzuu yakare musu kallo ya kece da kafira dariya, yace barka da zuwa mata masu neman biya bukata barka da zuwa fada boka duguzuu dan asarariya, me ke tafe da ku"? Umma hajara ta karkace kai tafara korowa boka bayani kamar haka Allah ya taimaki dan asarariya aljana inna ta dafe maka wannan da ka ke gani 'yatace sunan ta na'eema akwai wanda takeso saidai bata gabansa domin 'yar uwa ta da suke uba daya yakeso, shine mu ka zo a taimaka mata yaro yasota in ta kuma wanchan 'yar kishiya tawa ka hada ta da baqin jini ko kare banaso ya kusance ta da suna aure so nake tadawo tamkar mujiya a ciki'n tsuntsaye tadawo abun gudu ga samari boka duguzuu ya hagame katon bakinsa mai kama da tsohuwar salaga yana dariya, sai kuma ya koma yare sa da shi kadai yasan abunda yake fada kudaje nata shawagi a bakin'sa daga bisani tsit kamar ruwa yacinye shi, ya daga hannu'shi sama sai ga bakar leda akan tafin hannu'shi ya ajiye leda a gabansa, ciki'n muryar'sa mai kama da kukan Injimi markade yadakawa na'eema tsawa ke yarinya lallai kina da sa'a, a rayuwarki domin, inna tayi miki alqawali za ta nemo miki soyayya'r amar a tsorace na'eema take kallon shi jin ya anbace suna amar al'hali su basu fada masa suna sa ba boka duguzuu yacigaba da cewa ki kwatarda hankalinki nan da dan kankani lokacin za ki aure Amar ya kwance baqar leda da Ke gabansa yaciro laya karbi wannan ya miqawa na'eema hannu'ta na rawa ta karba yace wannan ki jefa ta cikin tsohuwar rijiya wannan kuma ki sakawa raheela cikin matashi da take kwanciya sai kuma wannan turare ki shafa a jikin kayan ki, sai kije wurin amar da ya shaki kamshi sa za rikice a son'ki zai rasa kwanciyar hankali har sai ya aure ki kuma zai tsani raheela tsana Mai tsanani gaske, abu daya zai warware wannan aikin shine in har ki kayi sake amar da raheela suka kwana a daki daya daga lokacin zai daina son'ki zai kuma tsane ki fiye da tsanarda yayi yiwa Raheela sai ki kiyaye na'eema tasauke ajiyar zuciya, umma ta zuge "zip" din "handbag" dinta ta fito da duk kudi'n da ke ciki ta zube su a gaban boka domin tasan wannan shine ka'ida sa tayi godiya suka fito daga bukkar kowane su ya jike da gumi suka dauki hanyar komawa gida zukata su cike da farin ciki don gani burin su zai cika. Raheela da Lantana na fitowa daga falon kaka, lantana ta mika mata sakon amar gashi likita yace a baki mtss......raheela taja tsoki tace dama kira da ki kace mamee nayi min kenan"? Lantana tayi murmushi, tace shine cikin zafin rai raheela ta fisgi takarda daga hannu lantana ta warware tafara karantawa kamar haka:-banaso ki dauki maganar kaka da mahimmanci cos" zuciyata tariga tayi zurfi a son'ki a dalilin baci rai da ki ka hadasa min yasa na wuce abuja batare da nayi ma kaka sallama ba ki kula min da kanki domin kinfi komai mahimmanci a wurina. "urs husband 2 b insha Allah Dr Amar matawalle. Raheela taja dogon tsoki ta cukuikuiye takarda ta jefa cikin flowers...... Jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:35 am] Jeeddah Aliyu🌹: [2:35PM, 5/9/2016] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~3⃣1⃣~ Lantana ta zaro ido hade da cewa haba uwa dakina wulakanci ba bu kyau, raheela ta yatsine fuska tace indai akan yaa amar ne wulakanci yanzu nafara sheka shi, amma Uwa dakina sai naga kamar hakan baidace ba ko ba komai likita dan uwa'nki ne don yana dan uwa'na shi zai sa na soshi"? Banaso yaa amar lantana saboda haka mu rufe "chapter" shi domin cigaba da zance'sa zai iya janyo baqin jini sa ya shafe ki, lantana takara zaro idanu tace Allah yabaki hankuri uwar dakina batare da raheela takara furta uffan ba ta riko hannu lantana tace zo muje "part" din mamee mu yi fira lantana ta tabe baki. A gajiye na'eema tayi parking din mota a lokacin daya suka balle kofar mota'r suka fito na'eema na jan kafa suka karasa cikin gida a "bedroom" din umma suka yadda zango umma hajara ta mayar'da ganinta wurin na'eema tace kin ga yanzu mu jefa daya'r laya a rijiya sauran aikin yarage gareki na'eema tayi murmushin mugunta tace anjima da dare zan je "part din kaka na cika saura aikin sai kuma yaa amar har dakinsa, zan kai masa ziyara umma hajara ta tintsire da dariya tace da kyau 'yar albarka sai yanzu nasan nayi kyakyawa haihuwa na'eema tace ae umma kyauwo 'ya tagaji uwarta sai yanzu nagano hali'n mutane gidanan da ki keyi min kashedi akai dama kamar jira umma takeyi ta wani gyara zama ta budewa na'eema sabon shafi na tugu da kisisina daga karshe suka fito babba falon inda aunty amarya take zaune hannu'ta rike da hisnul-muslim tana dubuwa, suka fara aika mata wulakantace kallo ciki'n sanyi jikin aunty amarya tadago idanu'ta mamaki ta yakaru sakamako gani na'eema na harara ta, kasa hankuri tayi tace lafiya ku ka tsaya min akai musanman ke na'eema naga kin zo min da wani bakon al'amari saboda ita wannan in da sabo na saba da halinta"? Ta nuna umma hajara da baki cikin hargowa umma hajara tace ke sadeeya hawainiya ki ta kiyaye rama ta domin ni kurugu ce mugun kifi duk uba da yaci tuwo da ni miya yasha aunty amarya tayi murmushi hade da cewa iko Allah yau kuma haukan ya motsa to sai kiyi da wani domin ni tun da kurciya ta banyi wannan hali'n dabbobi ba, ballatana yanzu da na ajiye iyali" na'eema tayi karaf ta karbe zance ta hanyar cewa ga ki nan katuwar dabba mai abun kunya to ki jawa shegiyar 'yar ki da ta za me miki annoba kunne ta fita gonata domin bakin rijiya ba wurin wasan makaho bane, tsantsan mamaki yarufe aunty amarya wai na'eema ce ta ke gaya mata haka shin me ke faruwa"? Maganar umma hajara ne ya katsiwa aunty amarya, zance zuci da takeyi in kuma taki zan jagorance tabarbarewa rayuwata domin zan mayar'da ita abun kwatance a gari in kunne yaji gangar jiki ta tsira. A harzuke aunty amarya ta mike tsaye tace, ba tun yau ba ki ke da wannan mumuna kudiri a ranki nagani kin tarwatsa rayuwa raheela to ta Allah ba taki ba "Allah ba zai baki sa'a ba bakar anniyar'ki kan'ki za ta koma, ke kuma na'eema wannan hanyar da ta daura ki akai ba hanyar kwarai bace domin tana so ta gurbata miki ingantaciya tarbiya da kaka tabaki, na'eema tayi mata kallon uku saura kwabo tace mahaifiya tace duk yadda taga dama tajuya akala rayuwa ta kuma duk ranar'da raheela takara yi wa umma rashin kunya,sai na rama mata akanki ke in takama ko dukanki zan iya domin anjima ana ruwa kasa tana shanyewa raheela ta jima tana ci wa mahaifiya ta mutuncin nima lokaci yayi da zan dauki famsa. Umma hajara tace da kyau iri albarka fada mata ba ita kadai ta iya haihuwa ba nima na haifa "aunty amarya tayi murmushin tare da cewa, duk rashin kunya da raheela ta ke yiwa mahaifiya ki bata taba zagin ta ba don haka kada ki sake kurciya ta dibe ki, ki zage ni domin hakan shi zai zame miki kuskure na karshe da za ki aikata a rayuwarki. Cikin fitsara mai cike da rashin kunya na'eema tace an zagi ki din munaf.....saura kalaman ta suka kargame a makoshi ta sakamako wawa mari da aunty amarya ta wanka mata, saida jin ta yadauke na wance gadi'n umma hajara tayi wani kukan kura tayi ciki'n aunty amarya, kamar za ta hadiye ta sai kuma taja tayi tsaye tana wani yarfe hannaye hade da durawa aunty amarya ashar gani zagin munisa yayi yawa yasa aunty amarya tashige dakinta, dole umma taja hannu na'eema suka koma inda suka fito umma hajara ta sauke ajiyar zuciya tace barni da shegiya kisan mumuke zan yi mata sai ta gwamace kida da karatu tashi maza kije dakin amar ki duba in yana nan kidawo ki shafa turare boka duguzuu, so nakeyi nafara cin uban mutane gidanan daya bayan daya na'eema tayi murmushin jin dadi ta mike tsaye tafita... [9:09PM, 5/9/2016] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~3⃣2⃣~ Kaitsaye ta doshe kofar dakin amar ta murda handling" taji kofar a rufe tayi shiru tana nazari ina amar yashiga ne ko yana "part" din kaka ba dan ranta yaso ba ta koma "part" dinsu domin tana tsoro shiga part" din kaka saboda tasan kaka na jiraye da ita a falon tarar'da umma tana cin abinci umma ta kalle ta ciki'n kulawa tace ya akayi ne"? Na'eema ta ya motsa fuska tace bayanan umma ta tabe baki tare da cewa shine ki kadawo maimako ki shiga "part" din fateema watakila yana chan ki san shi, da shegen nacin uwa sai kace shi kadai ne da. Da sauri na'eema takara miqewa tsaye, tafita daga falon da sallama tashiga falon mamee da raheela na ta faman kyalkyale dariya sakamako labari da Lantana take basu domin lantana gwanace a fagge ba da dariya, mamee ta katsi dariya da takeyi ta amsawa na'eema sallama takaraso ta gaida umma ta kuma watsawa raheela mugun kallo, mamee tace ina ki ka shiga ne na'eema"? Na'eema tayi murmushi tace na raka umma unguwa ne sai yanzu mu ka dawo tacigaba da cewa mamee ina yaa Amar naje daki'n shi naganshi a rufe"? Mamee tace amar ya tsofa a abuja saboda nasan shi da shagen gudu tsiya, na'eema tayi shiru yayida zufa ya keto kan fuskar'ta da kyar tasamu tayi "controlling" din kan'ta tayi wani dan maraye murmushi mai kama da yake, karaf suka hada ido da raheela ta wani galla mata harara ta mike tsaye tace mamee ni zan tafi batare da tajira amsa da mamee za ta bata tafita da sauri raheela, da mamee da kuma 'yar araka yarima asha kida wato lantana suka bi bayan na'eema da kallo kowane su da abunda yake sakawa a ciki'n zuciyarsa na'eema na shiga part din su tafashe da kuka tana zuwa tafada jikin umma hajara ciki'n yanayi na tashin hankali umma tadago ta tace to akoke sarki kuka me kuma, yafaru"? Ciki'n rashin mafita na'eema tace umma yaa amar ya koma abuja, shikenan narasa shi, da sauri umma tarufe mata baki tace maza ki tofe mugun yawu ko ta wane hali sai kin aure amar saboda haka gobe za ki dauki hanyar abuja domin aiwatarda shiri mu, na'eema ta zaro idanu tace haba umma wane irin zance ne kina nufi naje gidan yaa amar"? Umma tayi shu'umi murmushi tace gidan Suwaiba za ki yadda zango daga nan kanemi "hospital" din da yake aiki, ki bade shi da kamshi turare boka duguzuu, sai ki koma gidan Suwaiba ki jira sakamako domin banaso kidawo batare da maganar aure ba na'eema ta share hawaye ta tasaki murmushin samu nassara tace amma umma ke bala'e ce "brain" dinki na kawo "light" lallai ya zame mini dole gobe na dauki hanyar abuja. DARE******* Da misali karfe 8:30pm na dare raheela da kaka na zaune a falon kaka na Jan casbaha raheela kuma na dubu "book's" din'ta saboda gobe "monday tana da "test" na physics" wayar kaka da ke ajiye bisa hannu kujera tayi "ringing" kaka ta miqa hannuta bisa kujera tadauki wayar taddana kore madani ta kara a kunne ta tace "Assalamu alaikum" amar da ke kwance bisa "three star" a hadade falon shi da ke abuja yasaki murmushi yace "Wa'alaikum sallam" ya tsohuwa mai rai karfe ina fatar kina Cikin koshin lafiya"? Kaka tayi murmushin hade da cewa shakiyi banza ae ni banyi tsanmani magana za ta kara hada ni da kai ba, amar ya shafi murdadiya sumar'sa ya dan murmusa har "dimple" dinsa ya lotsa yace mai nema baya fushi kaka tun da ina son 'yar jikalle ki dole na shanye wulakanci ki. Kaka tayi 'yar bazawara dariya tace tanan kuma ka bullo to dadi abin bani na kai zomo ba rataya aka bani, amar ya tabe baki yace ke ji da wannan zaurance naki ni dai bata waya naji sanyayiya muryar'ta mai sanyaya mini zuciya ko nasami sukuni, kaka taja tsoki tace ba zan bayarba amar yayi kasa da murya cikin sigar rarrashi yace haba kaka ki taimaka min mana baki ga yadda nayi "missing" din'ta ji nakeyi kamar na zama tsuntsu na zo naga "beautiful face" din'ta. Kaka tace chan ta matsi maka kai da turanci ka domin ni bana fahimta abunda ka ke fada, Amar ya kyakyace da dariya daga bisani yace to bata waya in nagama soyewa da ita za ta fassara miki, abunda nake nufi "kaka takara kyabe baki tace kaji da shi, ta ciro wayar daga kunne ta tace ke raheela zo ki karbi waya ana so magana da ke ciki'n zumudi raheela ta taso ta karbe waya daga hannu kaka batare da ta duba sunan mai kiran nata ba domin tasan nazee ne kadai mai kiran'ta da wayar kaka ta aza wayar, bisa kunne ta tace "hellooo...nawan... Jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:35 am] Jeeddah Aliyu🌹: [12:51PM, 5/13/2016] Jeeddah Aliyu🌹: [8:41PM, 5/11/2016] Jeeddah Aliyu🌹: ￿￿￿￿🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆￿ ￿💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~3⃣3⃣~ Muryar'ta, ta daki dodo kunne amar ya wani lumshe idanu yace yaushe na zama naki"? Rass...gaban'ta yafadi sakamako jin murya da batayi zato da tsanmani kara jin ta ba da sauri ta sauke waya daga kunne ta, ta tsurawa suna shi da ke bisa "screen" idanu daga bisani ta maida waya'r bisa kunne ta, tace lafiya malam kace kaka tabani waya"?? Amar yayi murmushi hade da gyara kwanciyar shi, yace lafiya'r kenan "baby naa" dama so nakeyi nace miki na eso lafiya Mtss....taja tsoki tace to ni ina ruwa kaga malam kadaina yaudara kan'ka akaina domin ni bana son'ka kuma banaso kowace hulda ta hadani da kai, ran amar in yayi dubu yabaci sakamako jin furucin, raheela yasauke zazzafa ajiyar zuciya yace son'ki yariga yashiga zuciyata raheela duk bugu daya na zuciya ta hade yake da kwayar son'ki "I'm madly in love with you baby" ina roko ki da ki tausayawa rayuwata ki aure ni nayi, alqawali zan baki kulawa ta musanman wanda za yi sanadi da sona zai sami mutsugunni a zuciyar'ki. Ummh....dadi na kai yaa amar rashin fahimta da yare hausa fa nakeyi maka magana, nace banayi" banayi" yaa amar nace bana sonka tun da ba'a tare muka zo duniya ba don me da ba za ka kyale ni ba, so ba'a dole ka hakura ka nemi mai sonka. Runtsi idanu shi wasu hawaye masu masifar zafi da radadi suka zubo a gefen idanu shi suka sauka bisa wuya sa, yayida wani mashin yadaki zuciyar'sa da sauri yasaka hannu shi na hagu yadafe saitin da zuciyarsa,take tsananin son raheela yakara ratsa gangar jikinsa, da kyar ya tattaro sauran natsuwa sa ya kuma hada da Kafin hali'n domin shi kadai yasan hali'n da ya afka a ciki muryarsa na rawa yafara magana ina son'ki raheela amma zan bawa zuciyata hankuri ta hakura da ke amma kisani duk abunda yasame ni kece sila karo na farko da raheela ta ji tausayin amar yakamata, ta juya taga ko wane irin kallo kaka take aika mata saidai kash kaka bata wajen domin tun lokacin tabata waya tashige "bedroom" dinta tayi kasa da murya ciki'n tausasa halshe tace kayi hankuri yaa amar banaso kashiga wani hali a dalilina duk abunda nake fada maka har ciki zuciyata haka ne matukar yaya na'eema na numfashi a doron duniya na haramta a gare ka don haka ka rarrashi zuciyar'ka ta amince da yaya na'ee......"shut up" raheela yadaka mata mahaukaciya tsawa wanda ta hadasawa dodo kunne ta daukar zafi da sauri tasauke wayar daga kunne ta tasaka ta a "loudspeaker" yacigaba da magana cikin bacin rai da konar zuciya da alama ran 'yan maza yabaci kada Allah yasa ki soni raheela ni kuma nayi wa kaina alqawali kasancewa tare da ke domin ina sonki sannan kuma ko ta halin 'ka'ka sai na aure ki bakida mijin da yawuce ni amar matawalle. Batasan lokacin da tafashe da kuka ba domin lamari amar yafara bata tsoro mutum sai kace mahaukaci bana son'ka"bana sonka yaa amar kuma har abada bazan taba son'ka ba. Yayi murmushi takaici yace ba ki esa ba raheela wallahi baki esa kisa na zubar da hawaye na a banza yanda nayi kuka akan sonki dole ke ma sai kin zubarda hawaye ,akan sona koda ace banyi nassarawa aure ki ba sai nayi nassrawa cusa miki zazzafa soyayya ta yana karasa zance'sa ya katsi waya'r. Raheela tayi jefa da 'yar Nokia kaka ta bugi bango ta rabu gida biyu takarkare iya karfin'ta ta kwatsama ihu wayyo na shiga uku yaa amar zai kashe ni da gudu kaka fito daga dakin'ta har tayi tuntube saura kiris tafadi ta nufi wurin raheela da ke ta faman taratsin kuka Mai hade da ihu yau tsohon iskanci ta na da ya motsa a rikice kaka tariko ta, ta kuma girgiza ta da karfi'n gaske amma hakan baisa raheela tafasa abunda takeyi ba sai ma yakara mata karfin guiwa ta bude sabon babi na bori da hargowa na rantsa bana sonka yaa amar kuma kai baka esa kasani na so ka ba mugu kawai baqin azzulumi, na gwamace Jini jikina ya tsiyaye da zuciyata ta so ka, gani haukar ba mai karewa bace yasa kaka tarufe mata baki da tafin hannuta tace ke banaso shashanci banza da wofi kina hauka ne"? da za ki dinga yi min wannan kururuwa a gida, ture hannu kaka tayi daga bakin'ta tace ki yiwa Allah da manzon'sa kaka ki shiga tsakani na da yaa amar haka kawai ina Cikin kwanciyar hankali banida matsala asalima bansan miye damuwa ba saboda bantaba shiga cikin ta ba gashi yana yunkuri katsi mini jin dadi hade da farin ciki'na. Kaka tayi shiru tana nazari magana raheela daga bisani tace shikenan zan sam abin yi tashi ki je kwanta, raheela ta mike hade da kwashe "book's" din'ta na'eema da ke labe a bakin kofa tana saurare abunda ke wakana ta yaye "curtain" tashigo da 'yar siririya sallama kaka da raheela suka tsura mata na mujiya, daga bisani kaka ta balla mata harara tace me yashigo da ke bangare na"? Na'eema takara sunkuyarda kanta kasa tayi shiru, kaka tacigaba da fadar burin'ki ya cika na'eema raheela tace bataso amar, amma abunda ba ki saniba yanda raheela ta haramtawa kan'ta Amar haka shima amar ya haramta gare ki, ba tun yau nasha zaunar'da ke na gargade ki akan ki fitar'da soyayya amar daga ranki domin nasan akwai wace da ke zuciyar'sa amma da yake, ke mai naci tsiya ce ki kayi kunne uwar shegu da magana ta yanzu sai ki je ki zuba ruwa a kasa ki sha saboda raheela bataso amar kuma har abada ba zan taba amincewa ayi mata aure dole don haka ga ki ga amar dabara taragewa mai shiga rijiya, kaka na karasa maganar ta tashige dakin'ta ta bar raheela da na'eema a tsaye raheela ta kawo karshen shiru nasu ta hanyar cewa, ki yi hankuri yaya na'eema komai yayi farko yana da karshe nayi miki alqawali koda baki cikin, duniya na haramta ga yaa amar don haka ki kwatarda hankalinki dole yaa amar ya aure ki. Na'eema tayi murmushin mugunta tace na gode "my lovely sister" ta riko hannu raheela suka karasa "bedroom" dinsu suna shiga raheela ta ajiye "books dinta bisa "bedside drawer" tace yaya na'eema zan shiga wanka na'eema tadaga mata kai zuciyata cike da mugun nufi akan raheela tana gani tashiga "bathroom" ta mike da sauri ta nufi gadon raheela ta cusa layya ciki'n "pillow" ta ta ajiye pillow" ta kuma bisa nata gado, ta runtsi idanu'ta kamar tafara bacci nan take tafara hango kan'ta kwance bisa kirji yaa amar yana shayar'da ita ni'emataciya soyayya...... [8:30PM, 5/13/2016] Jeeddah Aliyu🌹: ￿￿🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆🍆￿￿￿ ￿💕Love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~￿3⃣4⃣￿~ Raheela na fitowa daga "bathroom" ta nufi "wardrobe" tafito da "sleeping dress" dinta sai Lokacin idanuta suka, sauka bisa fuskar na'eema da ke baccin karya, ta dan murmusa hade da cewa yaya na'eema badai har kinyi bacci ba"? Banza tayi da ita kamar da gaske din tayi bacci raheela ta sanya 'yar karamar "night gown" dinta "light blue" ta shafe jikin'ta da hadadiya humra kasancewa'r hakan ya zame mata jiki bata iya kwanciyar batare da ta wadata jikin'ta da Qamshi, na'eema da ke kallon'ta ta kasa ido a zuciyar'ta tace shegiya mai kama da karuwa ke ba Matar aure ba, amma kullum sai kin bade jiki da humra, duk lokacin da aikin boka yayi tasiri akanki za ki yi bayani da laranci, raheela tana gama abinda takeyi ta nufi gadon na'eema ta zauna kusa da ita tasoma bubuga mata hannu hade da kira sunanta yaya na'eema kitashi mu yi magana, ciki'n dacin rai ta tashi zaune tana wani yatsine fuska, a sanyaye raheela tafara magana yaya na'eema karki saka damuwa akanki domin inaji a jikina yaa amar yayi kusan zama mallaki'n ki na'eema tayi murmushin takaici tace raheela kenan wannan hasashe ne kawai ki keyi yaa amar ya sona ke yakeso don haka na hakura da shi, saboda ba zan iya cigaba da son namiji'n da ya ke son kanwa ta. Da sauri raheela tariko hannuta tana girgiza kai karki ki ce haka yaya na'eema nasan kinaso yaa amar so mai tsananin gaske bai kamata kiyi saurin "give up" a lokacin da yaa Amar ya fahimce ba zai taba samu na dole ya hakura ya karbi tayin soyayya ki. Na'eema tace kidaina wahalar'da yawun bakin'ki saboda na riga na fitar'da sonshi a zuciya'ta, raheela tayi murmushi jin dadi tace da kyau yaya na'eema taa dama Chan banaso ki aure shi, saboda bashida kirki kuma ga shi mugu, na'eema tayi murmushin yake hade da cewa ki je ki kwanta raheela dare yayi sosai kuma gobe "monday" kina zuwa "school" raheela ta mike ta nufi gadon'ta zuciyar'ta fass..sakamako ta shirya da 'YAR UWA TAA batare da wani tunani ba ta gyara "pillow" ta kwanta, na'eema nagani ta kwanta bisan "pillow" tasaki ajiyar zuciya dadi ya lullube ta nan take taji zuciyata wasai sai takeji kamar ta gama auren amar. Raheela na kwantawa bacci yayi awo gaba da ita dama akwai gajiya a jikin'ta don haka baccinta take shara ciki'n kwanciyar hankali. ABUJA******* Amar kwance bisa gadon sa abin duniya ya sha masa kai sai faman juyi yakeyi da "frame" mai dauke da "pic " din raheela yakara matsi "frame" din bisa kirjinsa tun lokacin da yayi waya da raheela yanemi natsu sa yarasa tabbas ina son raheela kuma ba zan iya rayuwa babu ita kuma sani da nayiwa iyayye mu ba za su amince da auren dole ba, to yanzu ina mafita"? Ya watsawa zuciyar'sa tambaya, dayan bangare na zuciyar'sa yace amar ka hakura da raheela domin ba rabo ka bace, a baiyane yace "No ba zan iya ba "cos raheela ta zama jini jikina bugun zuciya'ta haske idaniya ta "she is my whole life I can't do without her" ya runtsi idanu shi jin yakeyi tamkar yafashe da kuka sakamako zafi da radadi son raheela da ke yawon a sassa jikinsa, nan take yasoma danasani nunawa raheela kiyayya a maimako so duk yadafe kanshi da ke sarawa tamkar ana buga masa kuduma, ina sonki raheela zan iya aikata komai don na mallake ki, haka amar yacigaba da tsoki burutsu sa har barawo ya sace shi bai sami mafita ba. KADUNA******** Tana zaune Cikin "garden" hannu ta rike da "lollipop" tana tsotsa kamar wanda aka zungura ta juya tana kallon kofar shigowa ciki'n "garden" din umma hajara tagani tsaye fuskar'ta babu annuri, suna hada ido ta watsa mata harara ita ma raheela batayi kasa da guiwa ba ta murguda mata baki, ciki'n zalla zalunci hade da mugun nufi ta nufi waje raheela tace na jima ina jira zuwa wannan rana da zan kassara rayuwarki raheela, sai yau tsohon burin na yacika akanki kafin raheela tayi yunkuri bata amsa sai kawai tafito da wata kwalba tacigaba da cewa wannan "acid" ne da shi zan lalata miki jikin'ki ta yanda babu wani da namiji da zai yi sha'awa aurenki ta yanda za ki dawo abin gudu da kyama a wurin 'ya'ya maza, da sauri raheela tafara ja da baya tana zarar idanu, umma hajara na biye da ita tana kyalkyala dariya karaf taji tayi karo da mutum a bayanta a kidime ta juya sai kawai taga na'eema a tsaye fuskar'ta tafi ta umma hajara muni saboda ita har wani huce takeyi duk da haka raheela ta kankame ta ciki'n rawar murya tace yaya na'eema don Allah ki ce umma tayi hankuri kada ta watsa mini "acid" na'eema tayi mata wani mugun kallo ta ture ta daga jikin'ta fuskar'ta babu fara'a tace umma bani kwalba hannu ki da sauri umma ta bata tana juyowa ta watsawa raheela "acid" din wani masifafe zafi ya ratsa fatar jikinta tasaki gawurtace ihu a firgice ta falka tasaka hannuta tana share gumi rass....gaban'ta yafadi sakamako gani na'eema bata bisa gadon'ta da sauri ta dira kasa jikin'ta na rawa tafita daga dakin ta nufi daki'n kaka zaune tarar'da kaka bisa "pray mat" hannu ta rike da casbaha da gudu raheela takarasa waje'nta tashige jikin'ta kaka ta shafin kan'ta tasoma karanto mata addu'a tsari, saboda ta fahimci mumuna mafalki ne tayi ba'a dauki dogon lokacin ba bacci yakara awon gaba da raheela. WASHE GARI********* Tun misali karfe 8:20am driver yadauki hanyar abuja da na'eema suna shiga garin abuja "direct" gidan Suwaiba da ke wuse 2 ya wuce da ita batare da bata lokaci ba yajuya kaduna domin umarni da umma hajara tabashi kenan, ko hutawa na'eema batayi ba aunty Suwaiba tace tashi ku tafi ga Ramlat nan ta raka ki "hospital" din da yake aiki na'eema tabata fuska tace aunty bari na huta mana Suwaiba ta wulga mata harara hade da cewa ke fa sokowa mai nema baya hutu har sai yacima abinda yake nema tashi maza kutafi na'eema ta mike tsaye hade da saba "handbag" din'ta Ramlat ce ke driving" na'eema na zaune kusa da ita zuciya'rta cike da fargaba irin tarba da za ta samu daga wurin uban gaiya amar kaitsaye Ramlat tadanna hanci motarta a"Alliance hospital" da ke Garki inda amar yake aiki ta nufi "parking space tayi "parking" lokaci daya suka fito daga ciki'n mota Ramlat ta kalle na'eema tace kinsan "office" dinsa kuwa"? Na'eema ta girgiza hade da cewa bansaniba, Ramlat tace "okey ba matsala bari mu tambaya kaitsaye suka nufi ciki'n "reception" gaban na'eema na duka tara-tara waje wasu nurse da ke zaune suka nufa Ramlat tace tayi musu sallama daga bisani tace dan Allah "office" din Dr Amar m. Mawatalle mu ke nema Saida suka kare musu kallo sannan daya daga ciki'n su tace "steered" za ku bi wannan hanyar za ku ga "stairs" sai ku haura za ku ga hanya ta rabo kashe biyu dama da hagu to dama za ku bi "office" na uku shine office dinshi kuma za ku ga sunan Shi a jikin "office" din Ramlat ce tayi mata godiya suka bi hanya da ta nuna musu suna esa bakin office" din suka ja birki sakamako tsayarda su da "messenger" yayi yace akwai "patients" a ciki sai ku jira har tafito dole suka koma gefe suka tsaya "tsawon 10 minutes suka dauka a tsaye daga bisani "patients" din da ke ciki yafito, da sauri na'eema ta zuge zip din bag" dinta tafito da turare boka ta shafa a jikin'ta, da sauri hankali "messenger" yadawo kansu yasoma yi musu kallo tuhuma Ramlat ta fisgo hannu na'eema suka fada ciki'n "office" din..... {ina busy datz why ku ka daina gani "post din mijin yar uwa taa but insha Allah gobe zan kara wani post. thanks} Jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:35 am] Jeeddah Aliyu🌹: [12:26, 5/16/2016] Jeeddah Aliyu🌹: ￿￿￿￿🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆🍆 ￿💕love story 2016💕￿ Na Hauwa Shehu Aliyu🌹￿ ~￿￿3⃣5⃣~ Karaf idanu amar suka sauka bisa fuskar na'eema ciki'n baci rai ya mike tsaye yace "what's heel u are doing in my office na'ee....a hanzarce ya hadiye saura kalaman sa, sakamako tsarawa da kan'shi yayi da sauri yadafe kan shi ya koma ya zauna, ya tsurawa na'eema ido yayida ita kuma tana tsaye tana aika masa kallon kauna sai da tabbata amar yagama zuke Qamshi turare boka ta juya tafita da sauri Ramlat ta Mara mata baya amar da ke zaune ciki'n bako yanayi sai kawai ya tsince kan'shi da miqewa ya bi bayan'su{tsafi gaskiya mai shi} kallo daya za yiwa amar kagano baya ciki'n haiyyaci sa, gani yanda yafito a gigice yasanya "messenger" mikewa yace "doctor" lafiya nagan'ka a firgice"? Ciki'n sauri amar yawuce shi batare da yabashi amsa ba tun kafin yakarasa fita daga "reception" a kofar glass" ya tsinkaye shigar su na'eema cikin mota bai kara shiga tashin hankali ba saida yaga Ramlat tafigi mota ta nufi "gate" din fita daga "hospital" din ya bi motar da kallo yajuya da sauri cikin yanayi tafiyar masu karfi yakoma "office" din'shi kawai ya tsince kan'shi da hada komaitsa shi yafito "messenger" da ke tsaye cikin tsantsan mamaki, gani Dr Amar cikin wani yanayi da ya zame masa baqo bai gama mamaki sa ba sai gani shi, yayi yafito, da "briefcase" dinshi a rataye bisa kafada sa alama da ke nuna yatashi daga aiki kenan, amar bai damu da yanayi kallo da "messenger" yakeyi masa ba yaciro "key's" daga aljihu "coat" din da ke jikinsa yacilla masa hade da cewa ka rufe mini kofa ni zan fita, yana karasa zancesa yajuya da sauri yanufi "parking space" yashiga motar'sa yafice daga "hospital"din "direct" gidan'shi yanufa yana shiga falon ya jefar'da "briefcase" hade da wayoyi sa bisa kujera ya kuma cire "coat" ita ma ya jefar'da ita saida yadawo daga shi sai "white vest" sai kuma wando da ke jikinsa, jin yayi makoshi sa yabushe "fridge" yanufa yabude yadauko gwagwani "coke" ya balle kaifa kai saida, shanye ta tass sannan ya ajiye gwagwani'n akan "fridge" shiru yayi tafara nazari abunda yake ji game da na'eema a hankali ''brain" din'shi tafara aiki nan take yafara aikawa kan'shi tambayoyi marasa amsa shin me ke faruwa da ni"? Miyasa nakeji wani "feeling" akan na'eema"? Me na'eema ta zo yi abuja me kuma yakawo ta office dina"? Miyasa tun lokacin da ta tafi nake son Kara ganinta"? !oh god what's d wrong with me" kamar wanda aka mintsina yajuya yanufi "bedroom" yana shiga yawuce "bathroom" yasakewa kan'shi "shower" tsawon lokacin yadauka ruwa na zuba a jikinsa daga bisani ya kashe, "shower" yanufi wuri'n ajiye "towel" wayam ba towel" ko daya mtsss....yaja dan karami'n tsoki ciki'n rashin damuwa ya kwashi wando sa hade da farar "vest" dinsa yafito haka nan dama wannan na daya daga ciki'n al'ada amar duk lokacin da yayi wanka da yagama "using" da "towel sai yayi "flinging da shi tsakiyar daki in kuma yakara shiga wanka yafito da wani duk lokacin da yayi amfani da "towel" kasala mayar'da shi "bathroom" yakeji shiyasa, "bathroom" din shi za ka tarar'da "towel's" sun fi goma saboda baya iya mayar'da su mazauni su kaitsaye yanufi "wardrobe" yabude yafito "black jeans" da "red shirt" yasaka yanufi katon "dressing mirror" mai dauke da tarin "turaruka birjik yadauki turare "intense man" yafashe jikinsa daga bisani ya zura kafar'sa ciki'n "red boot" ya koma falo yafada bisa kujera hade da dafe kan'shi da yayi masa nauyi kamar an doura masa buhu'n "cement" zuciyar'sa tacigaba da zaiyano masa siffar na'eema, wani irin masifafe sonta yafara shawagi da sama zuciyar'sa yayida kasa'n zuciyarsa ke ta faman azalzala shi da son raheela, ya runtsi idanu shi da karfi nan take wani sashe na zuciyar'sa ya tilassa masa ta hanyar cewa lalle ya zame maka dole kanemi na'eema domin itace magani wannan damuwa taka, batare da yajira shawara daya'n sashe na zuciyarsa ya mike zubur yadauki daya daga cikin "phones" dinsa da ya watsar bisa kujera ya danno "number" na'eema. Tun lokacin da su na'eema suka koma gidan Aunty suwaiba su ka zube a, falon suna koro mata bayani abunda ya wakana tsakani su da amar muryar na'eema ce, takarade falon wato aunty sai yanzu nagano fa'eda da amfani da bokaye su ke da, kinga yanda yaa amar ya zuburo da sunan ya wanke min allo'na yana shaqar turare boka sai kawai yayi laushi har fa gudu sa yabiyo mu, tana karasa zanceta suka kyalkyale da dariya Suwaiba tace ae ni tun lokacin da aunty asabe ta hadani da boka duguzuu nadaina bin kowane boka in bashiba saboda aikinsa tamkar yanka wuka yake sha yanzu magani yanzu Ramlat da ke danna wayarta, sai Lokacin ta tsoma bakin'ta Cikin firar tasu domin ita kadai tasan yanayi da ta tsince zuciyar'ta ciki gaskiya momy da na'eema ba 'yar uwa ta bace da abunda zai hanani gwada tawa bajinta saboda "guy" ya hadu ba karya babban abinda yatafi da imani na "eye's" din'shi domin ko ciki'n bil'adam masu halitta irin na "eye's ball's" din'shi qalilan ne. Tun lokacin da Ramlat tafara zuzuta kyawo halitta amar kishi ya turnuke na'eema sai faman balla mata harara takeyi ciki'n fushi da daci rai ta bude baki za tayi magana waya'rta ta, katsi mata hanzari ta hanyar yin "ringing" da sauri ta zuge "zip" din "handbag" din'ta tafito da waya gani suna amar na yawo akan "screen yasa ta zunduma ihu hade da cewa wayyo dadi aunty Suwaiba yaa amar ne ya kira da sauri aunty Suwaiba tace maza ki daga mu ji abunda ya zo da shi na'eema ta yatsine fuska tace ba zan daga ba sai naja masa "class" aunty Suwaiba taja tsoki mtwww..tace ae yanzu bakida wani aji na'eema domin aiki'n asiri ne yake sarafa miki amar don haka karkiyi wasa da dama'rki ae kuwa da sauri na'eema tayi "receiving" ta aza waya'r bisa kunne ta kashe murya kamar Tsohuwa karuwa "hello yaa amar" Amar da ke kishigide da sauri yakoma zaune uhh...na'eema ya za ki yi min haka"? Me nayi maka yaa amar"? Hamm....yasauke ajiyar zuciya daga bisani ya tsince kan'shi da cewa kin tafi da zuciyata na'eema tun lokacin da idanu na suka hasko kyakyawar surar ki na nemi natsuwa da kwanciyar hankali na, narasa ki taimake dan uwa'nki domin a hali'n yanzu bana bukatar gani komai sai ke. ciki'n hanzari na'eema ta mike tayi hanyar fita daga falon, ciki'n tsanani jin dadi tace nima ina bukata gani ka yaa Amar domin zuciyata cike take da so da kauna'rka amar yashafi sumar kan'shi yace kina ina yanzu zan zo saboda ina bukatar lokaci na warware miki dinbi son'ki da ke zuciyata"? Ina gidan Aunty Suwaiba kanwar umma a "wuse 2 house No.6 shikenan gani nan zuwa yana karasa zance'sa yakashe waya yadauki "car key's" din shi yafice yashiga motar'sa kirar "Mercedes benz c-class" yafisge ta da karfi yanufi "gate" da gudu maigadi yafito daga dakin'shi ya bude masa "gate. *********************** KADUNA****** Tun da asuba da raheela tayi sallah ta koma bacci bata tashi ba sai misali karfe 8:02am, da sauri tafada "bathroom" tayi wanka agaugauce tasanya "uniform" ta dauki "school bag" din'ta tafito a falon tarar'da kaka tana saurare BBC" a 'yar karamar "radio ta raheela ta turo baki tace haba kaka shine baki tashe ni ba gashi har nayi kusan yin latti, kaka tayi murmushi hade da cewa sau nawa ina tayarda ke kina komawa bacci, raheela ta zaro ido tace shikenan bani kudi'na na "breakfast" nayi gaba kaka tace ki je daki ki dauka mana da gudu raheela takoma daki ta kuma tadawo da gudu tace nadauki 500 amma zan dawo miki da chanji Kafin kaka tabata amsa har takarasa fita daga falon bata ankara ba taji tayi karo da mutum, tana dago idanu'ta taci karo da nazeer tasaki ihu hade da cewa "oh shirt" nazeer yace "oh No" suka hada baki suka ce "oh yes" nazeer ya mika mata hannu suka tafa raheela tace yaya nazee yaukar yaushe yace da yamma amma na Lula ciki'n gari ban diro gidanan ba sai da tsakiyar dare raheela ta zaro ido hade da cewa guduwa kayi kenan"? Nazee yayi wani yarfe hannu yace kin ji ki da wani wai guduwa abu sai, kace dan "boarding school" raheela ta kyalkyale da dariya tace amma dai batare da izzini abba ko daddy kadawo ba"? Nazee ya tabe baki yace da izzini su nazo me zai sa nayi shigo gidanmu da tsakiyar dare ke bari na takaita miki labari ko su yaya Abdul basu san nayo kd ba. Raheela takara zaro idanu tace cab lalle yau da kai da daddy nazee ya yatsine fuska, hade da cewa share kawai tawan nima irin na yaa Amar zanyi bazan iya cigaba da aiki a karkashin "company" raheela tace uhh..kaji da shi ni dai mutafi ka kaini "school" bisa "bike" dinka nazee ya galla mata harara yace tun da ga "driver" ki yadawo ba to ba inda zan je a shagwabe raheela tace "please nawan wallahi yau test" nakeda kuma gashi nayi latti nazee yace mu tafi na sauke ki sarkin naci.... 🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~3⃣6⃣~ Amar na esa gidan Aunty suwaiba yayi "parking" a waje "gate" ya kira na'eema yace yana kofar gida ciki'n zumudi, na'eema tadauki mayafi'nta takara feshe jikinta da hadin turare boka, sai wani bahago kallo Ramlat take aika mata duk da na'eema taga yanayi Kallon da Ramlat take watsa mata sai tayi kamar bata ganta ba tanufi kofar fita tana wani, rausaya direct" waje motar'sa tanufa tun lokacin tafito amar yake faman kallon'ta yana kuma mamaki yanda ciki'n Dan kankani lokaci sonta yayi tasiri a Cikin zuciyar'sa tana karasowa ta bude kofar mota tashiga kamshi turare ta yabugi kofufi'n hanci sa, ya lumshe idanu daga bisani yabude Su ya watsa su bisa, fuskar'ta yayida na'eema ta rikice domin idanu amar suna daya daga ciki'n halitta shi, da ke tafiya da imani 'yan mata tace ina kwana yaa amar"? Hamm..,yasauke ajiyar zuciya hade da cewa kwana kuma na'eema ko dai bacci ki ke ji"? Ta wani rausayar'da kai cikin sigar kissa da kisisina tace a'a amar yadago mata hannu shi yace ki kalle agogo ki ga karfe nawa, yanzu ta tsurawa agogo nashi kirar "Rolex" idanu a baiyane tace 1:11p.m amar yayi shiru yana nazari abunda zai furta sai dai bashida zabi da yawuce ya furta domin jin yakeyi in har bai furta hakan ba ruhi sa zai iya fita daga gangar jikinsa don haka ya yiwa kan'sa kiyamullaili ta hanyar cewa na'eema gani nazo gare ki yau ba'a matsayin dan uwa ba nazo gare ki ne a matsayin masoyi na'eema ina son'ki kuma in har kin amince ina son mu raya suna ma'aki {s.w.a}. na'eema tasaki wani mushiriki murmushi na jin dadi tace na amince da kai yaa Amar dama Chan na jima jirgin son'ka yana yawo da ni kai ne ka so ka watsa mini kasa a ido, akan raheela, rass...gaban amar yafadi sakamako sunan raheela da na'eema ta kira sai kawai yatsince kan'shi cikin wani yanayi mai wuyar fassara, da kyar ya iya bude bakin'sa yace ki ajiye zance raheela a gefe "cos yanzu ke ce a gadon mulki zuciya'ta dadi yakara kashe na'eema haka su ka cigaba da fallasa asiri zuciya'rsu tsawo sati daya tayi a abuja babu abunda takeyi sai soyewa da amar. ****************** KARSHEN TIKA TIKA TIK*** Kamar yanda amar yasaba zuwa kaduna duk karshen mako hakan ce tafaru kasancewa yau juma'a karfe 12:03pm yatashi daga "office" direct gidan'shi da ke maitama ya wuce ya watsa ruwa ya chanza kayan zuwa wata tsadadiyar farar shadda galila yasaka bakar hula kubbe takalmin kafar'sa ma black" ne sai yafito tamkar sabon ango ga jikinsa na fitarda kamshi turare "natural vitality" kaitsaye yanufi "wuse 2" bai wani jima da tsayuwa ba na'eema tafito janye da 'yar karamar "trolley" din'ta da sauri amar ya balle murfi Mota yadunfare ta fuskar'sa dauke da murmushi ita ma ta mayar masa da martani hada su fari da ido ya karbi "trolley" din ya jefa a "seat" din baya ya kuma bude mata kofa tashiga ya zagaya yatayarda mota suka dauki hanyar kaduna tafiya ce akayi mai cike da firar so da kauna shiyasa suka dauki dogon lokacin kafin su eso garin kaduna, amar yadanna "horn" maigadi ya bude musu "gate" yanufi "parking" yayi parking" su ka fito daga ciki'n mota'r yayida amar ya kafe na'eema da fitinanu idanu shi, yace "sweety" ga mu a gida "Allah ya kawo mu lafiya da fatar in kinga umma ba za ki manta ni na'eema ta kada kwayar idon'ta tace matukar zan mantawa da kaina to zan iya mantawa da kai, yanzu ma don ya zama dole na shiga ciki don taga shedar nadawo lafiya ina esa mata da sakon aunty Suwaiba zan fito mu cigaba da firar mu mai sanya ni nishadi, ciki'n jin dadi amar yace shiyasa nake kara son'ki "sweety naa" bari nima na shiga na gaida mamee da kuma kaka. Rass-rass gaban na'eema yafadi saboda tasan matukar yashiga "part" din kaka dole sai yahadu da raheela ita kuma abinda batason faruwa shi kenan saboda tagani kamar amar in yahadu da raheela asiri zai daina aiki akan'shi tafin da amar yayi mata akan fuskar shi yayi sanadiyar dawowa da ita ciki'n natsuwa ta tunani me ki ke yi "sweety naa"? tambaya da amar ya watsa mata kenan ciki'n yanayi na kwarewa da yaudara tace banaso dai-dai da "seconds" daya ka yi min na nisanta da kai yaa amar don haka ka sanar'da daddy zance aure mu kafin ka koma kaduna. Amar ya dan murmusa yace angama sahiba taa da haka suka rabu ita ta nufi "part" din umma shi kuma yanufi "part din mamee. ******************** Da misali karfe 3:15pm achaba yasauke raheela a kofar gida yayi dai-dai da lokacin da amar yafito da motar'sa zai fita unguwa, karaf idanu shi suka sauka bisa fuskar raheela da ke sanye da "uniform" tana kachaniya fitowa da kudi daga aljihu wando ta tafito da naira dari ta mikawa dan achaba tace bani chanji cikin tsananin mamaki dan achaba yake kallon'ta yace wane irin chanji kuma, malama"? Raheela ta galla masa harara tace chanji da kasani ko kana nufi bakasan chaji ba"? Dan achaba yace "eh lallai yarinya kin zo da reni hankali na dauko ki tun daga "salvation" ki bani naira sannan kuma kice nabaki chanji dallah malama ki cika min kudi na raheela ta murtuke fuska tace kai kadaina yi min "shouting" ba fa abun hawa ne ba mu da a gidan'mu kawai nayi ra'ayi hawa achaba don haka kabani chanji na baka kudinka, tun lokacin da amar yaganta tasauka bisa achaba yayi "parking" yana kallon abunda ke faruwa tsakaninta da dan achaba cikin fushi da dacin rai ya balle murfi Mota yanufi waje ta fuskar'sa dauke da tsantsan kiyayya ta..... Jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:35 am] Jeeddah Aliyu🌹: [6:07PM, 5/18/2016] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕Love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~3⃣7⃣~ Tun kafin amar yakarasa waje su yaji muryar dan achaba yana fadar ke karki nemi ki kure mini maleji, nayi miki rashin mutunci kuma da Ki ke zance abun hawa, to uban wa yahana ki hawa abunda ku ke da, shi sai ki ka buge da hawa achaba dagani yanayi Zubi ki na 'yan aiki ne. Raheela ta zaro idanu hade da dakawa dan achaba tsawa kai mallam karka saki ka zage ni, kuma kudi'n ba zan ba yarba in kana da karfi ka kwata, kafin dan achaba yabata amsa amar yakaraso batare da ya kalli gefen da raheela ta ke ba yaciro 1000" ya mikawa dan achaba yayida raheela ta kawar'da fuskarta taki kallon sa da sauri dan achaba ya karbe kudi amar yajuya cikin salon tafiyar sa ta kasaita, dan achaba yace yallabai chanji ka, batare da yajuyo ba yace na barmaka raheela tabi amar da kallon mamaki, a zuciya ta tace me wannan mutumi yake nufi ne naga Sai wani shan Qamshi yakeyi"? ta tabe baki takara da cewa Chan ta matsi maka ta juya wurin dan achaba ta balla masa harara hade da cewa dallah malam ka ja rukubabe mashin dinka ka bar mana kofar gida dan achaba ya kyalkyale da dariya yace yanzu nan 'yan mata kiyi sa'a wannan balarabe yaya naki mai kama da ke saidai yafi ki hankali da natsuwa ya biyani kudi na da na gwada miki rashin mutunci mai "remote" bai jira jin ta baki raheela ba yaja babur dinsa yayi gaba. Raheela ta turo karamar kofa tashiga ciki'n gida da shigar'ta falon kaka ta jefar'da "school bag" bisa kujera tacire rigar "uniform" ta jefar tayi saura daga ita sai "vest" kaka dai na zaune tana kallon'ta da gudu tashiga "kitchen" sai ga ta da "plate" din abinci tana tafiya tana ci kaka ta girgiza kai tace wai raheela yaushe za kiyi hankali"? ta turo baki tace me nayi"? Kalli yanda ki ke cin abinci a tsaye kuma nasha yi miki fada kidaina wannan gudun naki na wahalar'da jini jiki amma kin ki dainawa, ta tabe baki tace shegiyar na debo kaka bakiji yanda hanji na yake tsuwa ba kaka tace ko yau kenan ba kiyi "breakfast" ba"? Raheela ta washe hakora hade da zaunawa kusa da kaka tace kaka bana fada Miki tara kudi nakeyi ba in lantana za ta tafi kauye na bata tasiyo mini awakai nayi kiyo, kisan tace awakai akwai arha a kauye'n su kudin da na tara za su iya siy......ke dallah dakata kaka ta taka mata birki tace miyasa bakida ta natsu raheela"? Ke kenan kullum da sabon iya shegen da za ki bullo da shi, ina murna kinfara hankali ashe sabuwar hauka nan tafe wance taci uban ta da. Raheela ta bata fuska ta ajiye "plate" kasa tace na fahimci tun lokacin da nace banaso yaa amar ki ka dauki zafi da ni shin kaka ko kindaina sona ne"? takarasa magana'rta kamar za tayi kuka kaka tayi murmushi tace raheela sarkin rigima yau kuma rigimar akaina tasauka, ki ajiye magana'r amar a gefe saboda tuni na rufe shafi'n ta ina ki kin ga wurin ajiye awakai a gidanan'"? Ciki zumudi raheela tace a bayan gida mana kuma ba wanda zai ce komai in har ki ka ce ke ce ki ka siya min. Kaka taja tsoki hade da cewa banaso zance banza raheela, in karki kuskure ki kara yi min zance awakai nan sai na saba miki. Raheela ta turo baki ta mike tsam ta tsallake "plate" din abinci tafice daga falon ta nufi "part" din'su tana shiga babba falon ta tarar'da umma hajara da na'eema a zaune suna kule-kulen makircin su dadi ya lullube raheela sakamako gani na'eema da sauri ta nufi kujera da na'eema da ke zaune tace lah''! Yaya na'eema yaushe Ki kadawo"? Ke miye haka wannan ae dabbanci ne da dakikanci miye hadi na da ke da za ki watsa mini wannan tambaya"? na'eema takarasa zanceta hade da ture raheela tafadi kasa bakin'ta ya bugi "stool" yashe sai jini ke zuba tasaka hannuta tadafe bakin nata a tsorace tadago tafara aikawa na'eema kallon mamaki, takara sauke ganinta bisa fuskar umma taga umma na murmushin mugunta, takara dawowa da ganinta wurin na'eema, kafin tayi wani yunkuri na'eema tacigaba da cewa wannan soman tabi ne ki ka fara gani mudi'n baki fita hanyar yaa amar sai na kassara ki domin amar nawa ne ni kadai. Raheela tasaki murmushin takaici tace haba!'' yaya na'eema yanzu akan da' namiji ki ka zabi ki watsar'da kaunar da mu ke yiwa junan mu"? Kwarai kuwa domin nafi kaunar shi akanki nafi so na rayu da shi akanki, ke yanzu ba komai bace a wuri'na face makiyiya na'eema na dinga aya a zanceta umma hajara tafara zazzaga nata, ina gargadi Ki da babba murya ki fita hanyar amar da na'eema, in kuma ki ka ki za ki sha dibin mamaki domin rayuwarki za tadawo tamkar ta alade. Da kyar raheela ta mike tsaye idanu'ta su ka cika da kwalla, ta kalli umma hajara ciki'n rauni murya tace, tabbas umma kinyi nasara datsa kaunar da ke tsakanina da na'eema, saidai kuma har abada ba za ki iya raba jini da ke gudana a jijiyoyi jikin'mu ba tun kafin na mallake hankali kaina nakeji wannan kazamar kalma daga bakin'ki amma kuma umma akwai abunda har izuwa yanzu da ki ka kasa amincewa da shi wanda har yanzu yake wahalar'da ke shine yarda da kaddara, in har baki manta ba kaka tasha fada miki cewa ni kainuwa ce dashen Allah, ba yanda za ki yi da ni dole ki rungume ta annabawa, domin da mugun alkaba'e ki yana tasiri akaina da yanzu bana numfashi a doron kasa. Ciki'n fushi umma tace karya ki keyi shegiya 'yar gadon talla shayi a wannan karon ni ce mai nasara domin na raba ki da amar rabuwa ta har abada ki kuma saurara zuwa bala'e da ke jira ki. Umma kenan ni yaa amar baya gabana koda ace ina sonshi zan iya sadaukar da soyayya da nakeyi masa ga na'eema ballantana banaso shi don haka ku je chan ku karata da shi. Wannan karo na'eema ce tabata amsa ta hanyar cewa, haka za ki qare babu Mashishini har abba yagaji da ke yasamu mai bakin uwa yabashi sadaka kuma ki bace mana da gani domin uwar'ki da ki ke takama da ita batanan sai ki koma inda ki kafito batare da raheela takara furta uffan ba tafice daga falon. tana fita daga falon tanufi "part" din kaka tana tafiya tana kuka, amar da ke tsaye a "compound" yana waya da Dr kb yadago da sauri sakamako sautin kuka raheela da yasauka ciki'n kunne sa ya tsura mata idanu har ta kawo kusa da shi yana kallon'ta ta raba gefe'nsa ta wuce tashige "part" din kaka ya bi ta da kallo yana so ya tambaye ta, me take yiwa kuka sai kuma yaji tamkar an dinke masa baki. Raheela na shiga falon taci karo da kaka zaune inda tabarta, gani yanda raheela take kuka yasa kaka cikin firgici tace ke lafiya kuka me ki keyi"? Ciki'n shashekar kuka raheela tace zamewa nayi a "bathroom" din aunty amarya baki na yafashe, kaka tayi murmushi tace kai raheela yanzu don kin zame shine ki ke wannan barar baki, ni har nayi tunani ko hajara ce ta taba min ke. raheela ta girgiza kai domin tasan matukar tafadawa kaka abunda yafaru yau mai rabata da umma hajara sai "Allah don haka sai ta yanke shawara da ta boyewa kaka asalin abunda umma da hajara su kayi mata. kaka ta rarrashe ta har tadaina kuka saidai kuma lebe bakin'ta na sama ya kumbure. ************************* WASHE GARI***** Amar yasami iyayye sa da zance na'eema daddy da Abba sunyi matukar farin ciki'n don haka su ka hada dan karami'n "family meeting" a falon kaka "daddy, abba, mamee, aunty amarya da kuma umma hajara gaba daya su suna zaune bisa kujeri falon kaka, yayida amar, nazeer, Abdulhakeem, Abdulhaleem, da na'eema suna zaune kasa bisan "carpert" raheela ce kadai ke zaune bisa kujera kusa da kaka. Daddy Yayi gyara murya yace hajja dama wani abin farin ciki ne yasamu yara nan amar da na'eema ne su ka hada kansu shine mu ga yadace a sanar'da ke saboda mu naso a hade su gaba daya har su abdul ayi biki'n kowa yahuta yajuya waje da nazeer yake zaune yace kai kadai yarage ka kawo mana wance ka keso, nazeer yayi murmushi da sauri raheela takara shigewa jikin kaka domin tasan itace zabi nazee kamar daga sama taji murya nazeer yana fadar...... [8:23PM, 5/18/2016] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~3⃣8⃣~ Nima "daddy nasami wance nakeso sunanta bahijja saidai ba mu gama fahimta juna ba saboda ban fi sati daya da haduwa da ita ba. Cabdijam tashin hankali wanda ba'a sa masa rana Cikin yanayi na tashin hankali raheela da kaka su ke kallon mutane falon, tuni jikin raheela yajike sharkaf da gumi'n yayida umma hajara tsantsan farin cikin ya baiyana akan fuskar'ta abba yace ba matsala nazeer sai kabani "address" din gidan su yarinya zan yi bincike akan'ta, ciki'n jin dadi nazeer yace toh abba. Daddy ne yafara angara da shiru da kaka tayi yafara yawa Cikin girmamawa yace hajja kinyi shiru ba ki ce komai ba"? Ciki'n tsanani fushi kaka tace ban amince da aure zumuncin ba don haka na soke aure tsakani amar da na'eema shi ya je yanemo matar'sa a waje ita ma taje tafara lalube mijin'ta a waje duk wanda ke Cikin falon ya girgiza da jin furucin kaka musanman amar da na'eema da kuma jahanama ga "passenger" umma hajara, Abba ne yayi yunkuri neman Karin haske daga wuri'n kaka yace hajja ba mu muka hada su ba su ne suka hada kansu kaka ta zaro idanu ta masu cike da masifa tace kai Abdullahi ka kiyaye ni banaso maganar banza duka'nku a karkashin iko na ku ke kuma ba wanda ya esa ya zantarda wani hukunci batare da amincewa ta don haka ku tashi ku bace mini da gani munafuci banza da wofi duk wani munafuki, ina sane da shi a gidanan sai nayi magani shi nace ku tashi ku fice daga falon kaka takara daka masu tsawa, da sauri mamee da aunty amarya su ka fara mikewa suka fice umma hajara ma ba'a bar'ta a baya ba ta Mara musu baya zuciyar'ta cike da haushi takaici kaka yayida "daddy da Abba suka bi ayari su abdul suka fice yazamana saura amar da na'eema da suka fita haiyyaci su sai kuma raheela da ke sharar hawaye a fakace kaka tajuya waje na'eema ciki'n hargowa tace ke tsohuwar makira me ki ke jira ne da ba ki bacewa ganina ba"? A hargitsi na'eema ta mike tafice amar ya mike kamar ragumi, kaka ta galla masa harara hade da cewa koma ka zauna tsoho algugumi mai baki biyu, ciki'n tashin hankali raheela ta tashi tafita daga falon yayida amar ya bi ta da kallo, kai....kaka tadaka masa tace daina kallon'ta in baso ka keyi na tsiyaye maka kwayar ido munafuki kawai da sauri amar ya sunkuyarda kai falon yayi shiru na tsawon dakika biyar daga bisani kaka tasoma kare masa kallo tace amar kadago idanu ka ka kalle na da kyau domin zan fi gansuwa da amsa min tambayoyi na da za kayi ciki'n faduwar gaba amar yadago, fuskar'sa kaka tacigaba da fadar yaushe kafara son na'eema"? Yaushe ne kuma kadaina son raheela"? shin dama chan raheela ka ke so ko na'eema"? Ko kuma gaba daya su ka ke so"? Kuma yazame maka dole ka amsa mini wadanan tambayoyi. Kaitsaye amar yatsince kan'shi da fadar nafara son na'eema tun kafin ta mallaki hankali kan'ta cikin mamaki kaka ta katsi masa hanzari ta hanyar cewa na'eema ko raheela"? Ciki'n rashin damuwa Amar yace na'eema nake nufi kaka tayi kyaci ta wani girgiza kai, amar yacigaba da fadar sai kuma amsar tambayar'ki ta biyu bantaba son raheela ba asalima na tsane ta fiye da tunani kuma kema sheda ce akan haka, kaka takara harzuka ta cika fam jira take wani mai tsantsayi yatabata ta fashe, amar yace sai kuma ams...kai saurara bana bukatar jin wata amsa daga bakin'ka, badai na'eema ka keso ba kuma baka taba son raheela ba to tashi kafita, kamar jira yakeyi ya mike yafice daga falon. Kaka ta share gumi'n da ya wanke mata fuska tasoma zance zuci shin meke faruwa da amar da kuma wannan dan banza nazeeru tabbas nasan amar yana so raheela nazeeru ma yana sonta amma kowane su ya kasa furta hakan agare ta nan take wani irin tsoro ya lullube kaka tafara addu'a domin ita kadai ce mafita agareta har raheela tashigo kaka na duniyar tunani da karfi ta girgiza kaka tadawo haiyyaci ta Cikin sanyi murya raheela tace kaka kinga yanda yaya nazee yayi min koh"?ashe dama yana da wance yakeso yaudara ta ce kawai, yakeyi. Kaka ta girgiza kai ciki'n takaici tace ae ba ke kadai aka yaudara ba raheela nima amar ya yaudare ni raheela batasan lokacin da ta kyalkyale da dariya nan take taji bacin rai da ke ranta yafita taji zuciyata wasai kamar an wanke mata da soso ta takaita dariya da ke yi tace dama chan kece ba ki fahimci hakan ba kowa yasan tsakanina da yaa Amar kiyayya ce mai zafi yabijro da wannan zance ne don kawai yabata tsakanina da yaya na'eema kuma yayi nasara don haka ina roko ki kaka da ki danne zuciyar'ki kiyi hankuri ki amince da aure su kada ki kawo kace-nace a zuri'ar ki Yaya nazee da nakeji dan sonshi a zuciyata shima yanzu naji nadaina sonshi ki amince kawai kaka kowa rai yayi yiwa dadi bai yi kamar mai shi, ba ki zuba na mujiya ki sha kallo. har raheela tadasa aya a zanceta kaka tana yi mata kallon mamaki kasa hankuri kaka tayi saida ta furta abunda ke ranta ashe dai raheela kinfara hankali, raheela takara kyalkyalewa da dariya kaka tana taya ta daga bisani raheela tace dama ina da hankali kaka tsabar iya shege ne kawai irin na wanda yake da goyon bayan kaka irin ki kaka takai mata duka hade da cewa ja'ira anjima zan nemo iyayye naki nafada musu na amince da aure'n ciki'n tsanani jin dadi raheela ta rungume kaka. **************** DARE****** Da misali karfe 8:30 na dare kaka ta kira daddy da Abba ka kalle su, daya bayan daya tace na amince da aure 'ya'yanku Allah yasanya alkhairi Cikin tsananin jin dadi Abba da daddy suka ce "ameen!'' Daddy yacigaba da cewa nan da wata daya za'ayi bikin su kowane su yayi azumin da iyalinsa. Kaka tace uhh..Allah yanuna mana yayida abba da daddy" suka cigaba da tsara yanda bikin zai kasance kaka jin su kawai takeyi gani yanda ta zuba musu na mujiya yasa suka suyi mata sai da safe.... jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:35 am] Jeeddah Aliyu🌹: [11:45PM, 5/19/2016] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~3⃣9⃣~ Raheela cikin ''uniform'' din'ta na isalamiyya tafito daga "bedroom" din kaka saboda tun lokacin da na'eema tayi musu kaura ita ma ta tattaro shirginta tadawo daki'n kaka da zama takaraso cikin falon kaka na zaune idanuta kyan bisa akwati talabiji tana kallon manara tv" raheela tace kaka na tafi isalamiyya sai lokacin kaka ta dauke, idanu ta daga talabijin din ta kalli raheela gani tana tsotsa "lollipop" yasa kaka ta galla mata harara hade da cewa ba dai hanya za ki bi kina tsotsa duniya bisa tsinke ba"? Raheela ta kyalkyale da dariya tace kai wallahi kaka kina da abin dariya, "lollipop" ake cewa ba duniya bisa tsinke ba'' kaka ta tabe baki tace duk daya ne raheela ta juya nufi kofar fita tana fadar sai nadawo kaka tace in ki ka kuskura ki ka bi hanya kina tsotsa duniya bisa tsinke nan ni da ke. Takara kyalkyalewa da dariya tace da na kai "gate" zan cire na yarr kaka tace da yafi miki, raheela na fitowa ta hango yaa amar a bakin kofar dakinsa yana waya kallo daya tayi masa ta kawar'da fuskarta a zuciyata tace shi wannan mutumi bashida aiki'n yi sai waya sai kace tsohuwar karuwa, da wannan zance zuci ta nufi "gate" tana kai wa gate" ta yiwa "lollipop" din bakin'ta tauna daya ta jefar'da tsinke ta bude kofa tafita. Waya amar yakeyi amma gaba daya hankali'nsa yana wuri'n raheela a zuciya'rsa yace ita wannan ko me takeji a cikin "lollipop" !oho" yana ciki'n waya ya hango na'eema ta nufo waje'n sa fuskar'ta dauke da murmushi shima ya mayar mata martani, tun kafin takaraso ya katsi waya'r da yakeyi. Ciki'n shagwaba tace yaa amar laifi me nayi da yau duk baka nemi ganina ba"? Ko bakayi farin ciki da amincewa da kaka tayi na aure mu"? Ya dan murmusa ciki'n yanayi na wanda bayaso yawan surutu yace wadanan tambayoyi duk a lokacin daya na'eema wane daga ciki zan fara amsa miki"? Tayi wani fari da ido tamkar na wance akayiwa gyaran idanu, ita a dole sai ta burge amar tace gaba daya za ka amsa mun. Ya tabe baki yace uhmm...na'eema kenan mu ajiye zance wadanan tambayoyi naki a gefe ki fara amsa mini nawa tambaya miyasa baki tafi isalamiyya ba"? Na'eema ta yatsine fuska hade da cewa ni da zanyi aure me zan je dauka a isalamiyya. Kallon mamaki amar yakeyi mata daga bisani yace wannan ba dalili bane na'eema" aure da sai nan da wata daya za'ayi ba zai zama dalili'n da zai hanaki zuwa isalamiyya ba. Na'eema takara yatsine fuska har da wani turo baki tace banyi ra'ayi zuwa ba, amar ya tsura mata idanu daga bisani yace shikenan yanzu ina ki ka nufa"? Ta wani langwabe kai tace zuwa nayi mu fara tsara yanda biki'n mu zai gudana, amar ya gyara tsayuwa sa yace inajinki dama cewa nayi ka tura mini kudi ta "account" dina "next week" mu tafi "Dubai" ni da umma da kuma aunty Suwaiba mu hado kayan lefe na. Har ta dasa aya a zanceta Amar yana kallon'ta yayi dan bazawari murmushi yace ba matsala amma ki bari sai nafadawa mamee da kuma aunty amarya in har sun amince da hakan ko nawa ki ke da bukata zan tura miki. Wani katon haushi ya turnuke na'eema sakamako sunan aunty amarya da amar ya kira da kyar tayi "controlling" baci'n ranta tasaki murmushin yake tace amma yaa amar miye fa'eda fadawa aunty amarya"? Amar ya dubi agogon hannu sa yaga har 6:30 tayi a zuciya'rsa yace me ya tsayarda raheela har yanzu batadawo ba"? Wani bangare na zuciyar'sa yace kai amar ina ruwan'ka da ita, kamar daga sama yaji muryar na'eema tana cewa yaa kayi shiru baka ce da ni komai ba"? Ya lumshe idanu shi daga bisani ya bude su yace "please na'eema we'll talk about it later okey" Na'eema tace amma kum....da sauri ya katsita ta hanyar cewa lokacin sallah yayi ki shiga gida Batare da yajira jin ta bakinta ba yanufi "gate" yayida na'eema tabi bayan shi da kallon mamaki. kaitaye amar yanufi masallaci yayi sallah magarib, liman yana sallamewa ko addu'a amar baiyi ba yafito daga masallaci'n sakamako wani zafi da yake ji zuciyar'sa nayi yanufi bakin titi shagon sayar'da kayan masarufi yashiga ciki'n sakin fuska mai shago ya gaida shi daga bisani yace me za'a kawo yallabai"? Kawai amar ya tsince kan'shi da fadar sigari nakeso mai shago yace wace iri yallabai'"? Amar yayi shiru saboda shi dama ba shan ta yakeyi ba sai in tayi masa dadi ko kuma in yana ciki'n damuwa da ya dan busa ta sai yaji sauki damuwar'sa in kanada "oris" kabani kwali'n daya ka kuma hada mini da "lighter" Mai shago yace toh..yallabai shikenan za'a kawo"? Kamar daga sama amar ya tsince kan'shi da cewa ka hado mini da "lollipop" Toh..yallabai "cartoon" za'a kawo ko kuma jakka"? Kaitsaye amar yace "cartoon" saboda yafara gajiya da tambayoyi mai shago. Gani mai shago yajuya ciki'n shagon yasa Amar ya mayar'da hankali'nsa waje'n titi raheela ya hango ita da kawar'ta zainab za su tsallako titi hakan ne yabashi damar karewa raheela, kallo yayida kasan zuciyar'sa yake bugawa da sauri da sauri yana kuma jin wani abu yana masa yawo a jini sa murya mai shago ce ta dawo da shi daga natsuwa shi yafito da kudi daga aljihu wando "jeans" din da ke jikinsa ya mikawa mai shago kudi ya karbe kayansa yajuya. Da sauri zainab ta zugure raheela tace ke nayi miki farin gani takarasa magana tana dariya. Raheela tayi murmushi hade da cewa wa ki ka gane mun 'yar uwa"? Cikin dariya Zainab tace "Hero" Mtwww....amma Zainab ke banza ce wallahi ki karasa abunda idanu ki za su hasko miki sai yaa amar, zainab ta kyalkyale da dariya tace wai raheela yaushe za ku daina 'Yar tsama da ke da "hero"? Ba rana "because I hate him" Ni da za ki dauki shawara na da nace da ya aure yaya na'eema ki hada 'yan komaitsa ki a "Ghana most go" ki tare gidanshi kina musu wanke-wanke da shara. Har Zainab ta dasa aya raheela na watsa mata harara daga bisni tace "god forbid" koda zan yi shara da wanke-wanke ba dai a gidan "hero" ba. Amar tafiya kawai yakeyi da gangar jikinsa amma zuciyar'sa bata tare da shi jin yakeyi kamar yajuya yakara kallon fuskar raheela sai kuma yaji wata sabuwar tsanarta na kara shiga'rsa da sauri ya tura kofa yashige cikin gida "cos bayaso kara gani fuskar raheela saboda tana jefa sa cikin yanayi na kila-wa-kala. Raheela ta tura zainab cikin gida'nsu da yake tsakani gidan su zainab da na su raheela gidaje uku ne yaraba su "oya shiga gida kice kuma ina gaida mama. Zainab tana dariya tace yau kawata har da kora na"? "Eh na kore ki din" saboda na fahimci rashin kirki yanaso motsawa. Zainab tace "Allah ya huci zuciyar raheela ta yaa amar "d real hero" Raheela taja tsoki hade da cewa Allah ya esa tsakanina da ke kuma daga yau muraba hanya da ke tana karasa zanceta tajuya fuuu..alamar tayi fushi zainab tafara kwalla mata kira raheela"raheela " please I'm sorry daina tsaya na fada miki wata magana mai dadi" gani Zainab ta biyo ta yasa ta kwasa da gudu tana kai wa kofar gida ta ban'ki "gate" tashiga gida, amar da ke tsaye a kofar dakinsa yana jiran tsanmani yadago a firgice yana kallon raheela maigadi da ke zaune bisa farar kujerar roba yace sannu da dawowa katafila sarkin aiki ki tausayawa wannan kofar mana kalle yanda tadawo duk ta dalilin ban'ka da ki keyi mata na tabbata wannan "gate" ko shekara ba zatayi ba alhaji zai chanza ta saboda gaba daya kin fitar'da ita daga haiyyaci ta. Raheela ta ya motsa fuska tace banaso sharri baba duk mutane, da ke shigowa gidanan ta sama suke shigowa ni kadai ce nake bi ta gate"? Maigadi, yace ke kadai ce dai mai shigowa da gudun bala'e sai kace kura ta ya biyo ki. Wani kallo raheela ta watsawa maigadi ta juya ta shige "part" din kaka batare da ta Kalli amar da ke tsaye yana tunani mafita.... [4:36PM, 5/20/2016] Jeeddah Aliyu🌹: ￿￿🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆🍆￿￿￿ ￿💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~￿4⃣0⃣~ Sai da yadauki tsawon 10 minutes" a tsaye daga bisani ya yankewa kan'shi shawara da za ta fisheshi, "part" din kaka ya nufa cikin yanayi na mutumi da ke ciki'n tsantsan damuwa yayi sallama. Sani daraja da sallama take da yasa kaka ta amsa masa a dakile kaitsaye yanufi kujera da ke "facing din kaka ya zauna ya wani murtuke fuska, ita ma kaka ta kwabe ta ta fuska jin takeyi kamar ta rufe amar da duka sakamako dan banza haushi da yake bata. Raheela tafito daga "bedroom ta sauya kaya zuwa "gown ta "slink material" kan'ta babu dan kwali'n tana gani amar saida gaban'ta yafadi kawai ta fuske takarasa shigowa ciki'n falon, tace da shi ina wuni yaa amar"? Saida ya gama shan kamshi sa ya amsa mata chan kasan makoshi "lafiya qalau" daga haka raheela ta juya waje kaka tace kaka ina ki ka ajiye min 'yar karamar jakkar nan da nake saka "comb's" dina a ciki"? Ki duba ciki "drawer" gefen gado har raheela ta juya amar yace ke in da akwai fura ki kawo min kuma kisaka kankara a ciki raheela tajuyo tana masa kallon mamaki sakamako gani yanda ya wani lafe jikin kujera kamar ba shi bane yayi magana, a fusace kaka tace taki ta kawo maka fura ae ba ajiye ta kayi ba in har kanaso fura kaje ka bude "fridge" da kan'ka kadauka munafuki kawai mai baki biyu. Amar ya juya ya, kalleta ya ga yanda take huci kamar za ta rufe shi da duka ya yi murmushi sannan ya fara magana "haba kaka duk wannan bacin rai na menene tsakani jiya da yau narasa gane kan'ki"? Ae kuwa kaka takara fusata ciki'n takaici tace kai abdulrazaq kafita daga ido na, na rufe ko ubanka bai esa ya rena mini hankali ballatana kai haihuwa jiya. Amar ya zaro idanu hade da rike baki Yace cabdijam!" lalle abin yau babban ne da baki'nki kaka ki ke, fadar abdulrazaq, kaka ta yi doguwar ajiyar zuciya kamar za ta hadiye zuciyar'ta saboda takaici'n amar" tace nace abdulrazaq uba na ne da zan ji shakku fadar sunan"? Uhhm...Allah yabaki na mai bara ni fura na zo sha ba neman masifa ba, yajuya wurin raheela, da ke tsaye tana kallon'su ya doka mata tsawa ke dallah wuce ki je ki kawo mun aike da na yi miki tun kafin jikin'ki yafada miki'' a razane raheela tafada "kitchen" kaka ta galla masa harara hade da cewa maras zuciya kawai, amar ya tabe baki ya Mike tsaye hannaye shi, zube ciki'n aljihu wando sa, ya nufi kusa da inda kaka take zaune ya dan rankwafa kamar mai rada yace "SO tsuntsu ne kaka a yanzu tsuntsun son raheela yatashi daga kan'ta ya koma kan na'eema don haka kidaina wannan masifa taki saboda ba shi zai sa nadaina son na'eema ba ko kin manta lokacin da kambu sarauta zuciya'ta yake hannu ta wulakanci da tadinga yi min nima yanzu nasami mai sona ita ma ta je ta nemi mai sonta. Ciki'n zafin rai kaka takai masa duka tasami shi a kafada, da sauri ta yarfe hannuta amar ya kyalkyale da dariya Keta yace, kai wannan tsohuwa akwai ki da rigima za ki kar'ya hannu ki a banza Ki janyowa 'ya'yanki aiki. Ran kaka yakara baci masifa da bala'e ta suka kara motsawa, dai-dai lokacin da raheela tafito da ''jug a hannu ta amar ya juya waje ta yace Ke"! Ki kai min dakina kuma ki ka bari nariga ki fita falon nan sai nafasa miki baki, yana karasa zance'sa yafice. raheela tayi narai-narai da ido kamar za ta fasa kuka tace kaka dan Allah ki shiga tsakani na da wannan baqin azzalumi, kaka ta gyara zama tace jeki ki kai masa furar in har ya cika tantiri ya tabaki yaga yankar kauna gangariya. Ciki'n sanyi jiki raheela tafita saboda ita kam yanzu tafara tsorata da lamari yaa amar tana zuwa bakin kofar dakinsa taja tayi tsaye tana tunani yanda za tayi tashiga, dakin nasa, kamar daga sama taji murya'rsa yana fadar wai uban me ki ke jira a bakin kofa"? a firgice tafada ciki'n daki'n jikin'ta na rawa sai kace mazari ta dire masa "jug din fura bisa "stool shi kuma sai faman harara ta yakeyi har tajuya ta nufi kofa yace ke"! Zo nan da sauri raheela tadawo yanuna mata kwali'n da ke ajiye kusa da kafafu sa ciki'n esa da takama yace dauka ki tafi da shi, jikin'ta na rawa tadauki kwali'n yaa amar wa zan kaiwa"? Harara ya balla mata duk fadin gidanan wa ke shan "lollipop"? Ni"! Tafada a takaice' saida ya wani ya motsa fuska yace to na ki ne kuma duk ranar'da nakara gani ki ba dan kwali' sai na yanke wannan gashi da ki ke yi wa mutane yanga da shi "understood"? a tsorace ta daga kai, oya fita ki bani wuri da sauri tafice har tana tuntube da takalmin shi ya bi ta da kallo mai cike da wuyar fassarawa. ************************** SAURA SATI UKU******* A wannan lokacin biki ya rage saura sati uku, alhaji Abdullah matawalle zaune ciki'n falon shi, raheela na zaune kusa da shi, sai faman buga "game" takeyi da waya'r abba nata, umma hajara tashigo fuskar'ta a murtuke na'eema na bayan'ta saida ta gallawa raheela harara, sannan ta nemi wuri ta zauna na'eema ta zauna kusa da ita ba su fi dakika biyar da zama aunty amarya tashigo ita ma wuri ta nema ta dosana duwawu ta, alhaji Abdullah ya yi gyaran murya yace dalilin da yasa na tara ku a nan inaso naji abunda ku ke da bukata na biki"? Karaf umma tace ni babbar damuwa ta bai wuce har aure yarage saura sati uku amma har yanzu amar bai kawo lefe ba, tun lokacin da tafara magana abba yake watsa mata mugun kallo daga bisani yace ke fa hajara bakida hankali, yanzu don tsabar wauta irin naki amar ne zai kawo kayan lefe a gidanan kenan ba aure zumuncin za'ayi masa ba umma ta zaro idanu tace kutt..ae kuwa ba zata sabu ba bindinga a ruwa to in bai kawo kayan lefe ba me za ta saka a lokacin biki"? Ta fita tsirarai abba yafada ciki'n baci rai, akan wannan mugun hali'n naki yasa hajja tace bata amince da aure zumunci ba in har kina so zama lafiya karki kara yi min zance lefe, abba yana karasa zance'sa yafice ciki'n fushi raheela tace abba wayar'ka batare da yajuya ba yace ki kai min mota mama naa!" raheela ta mike tsaye ta kalli umma hajara da na'eema gani yanda umma take huci yaba raheela dariya batasan lokacin da ta kyalkyale da dariya, ae kuwa umma ta zabura tafara zagin raheela ciki'n mummuna furuci ba dai ni ki ke yiwa dariya ba wallahi sai ta zame miki kuka shegiya bakar tabataciya sai na wulakanta rayuwarki, da sauri aunty amarya ta yo kan raheela da suna ta yi mata wawa'n duka da gudu raheela tafita amma don tsabar daukar magana irin na raheela saida ta juya ta yiwa umma gwalo hade da cewa umma mai kayan lefe, ta falla da gudu ta yi tafiyar'ta, aunty amarya na gani haka tafice daga falon yayida umma da na'eema su ka cigaba da aibanta raheela..... Jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:37 am] Jeeddah Aliyu🌹: [11:00PM, 5/21/2016] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~4⃣1⃣~ BIKI'N BIDIRI****** Yau ta kasance ranar daurin aure amar da na'eema kofar gidan alhaji muh'd matawalle da dan uwan'sa alhaji Abdullah matawalle yacika babu masaka tsinke da misali karfe 2:30 na rana aka daura aure amar da na'eema a bisa sadaki naira dubu hamsi wanda alhaji Abdullah yabiya a matsayin shi na uban ango kuma waliyan sa yayida alhaji muh'd yakasance waliyin amarya, bayan kamalla dauri aure da misali karfe 3:00 akayi cin abinci liyyafa kowane ango ka kalli fuskar'sa na dauke da tsantsan farin ciki na gani wannan rana mai albarka sabani amar matawalle da fuskar'sa take murtuke sai kace maigadin makabarta, yanayi sa tamkar na wanda aka aikowa da sakon mutuwa kallo daya za ka yi masa kagano akwai boyayye al'amari a tare da shi saleem ya kalli su abdulhaleem da ke ta fama, washe hakora da ke nuna yau ranar farin ciki'n su ce, yace "bros wai me ke damu yaa Amar ne naga kowa yana annashuwa banda shi miye matsalar shi"? Abdulhakeem yayi ajiyar zuciya hade da cewa nima na fahimci akwai abunda yake damu shi yanayi sa sam baiyi kama da na ango ba, sadeeq ya dan murmusa yace kodai su abba ne suka hada shi da na'eema"? domin wannan yanayi da yake ciki yanayi na wanda aka yiwa auren dole, nazeer ya kyalkyale da dariya yace lalle bakasan waye yaa Amar ba wannan shu'umin ne zai amince da auren dole"? Abdulhakeem yace "uhhm.. shi dai akwai abunda yake damu shi, kuma na tabbata koda ace za mu tambaye shi ba lallai bane ya fada mana damuwar sa kawai mu tayi shi da addu'a "Allah yaye masa abunda yake damu sa, nazeer yace wannan shine taimako da za mu iya masa a matsayin mu na 'yan uwan sa. da wannan sharhi suka rufe zance yayida kowane su yacigaba da sabgar gabansa. Da misali karfe 5:30 na yamma amar yana zaune a "parking space" da sigari a hannu shi, yana zuka a hankali idanu shi sun kada sun yi jajir zuciyar'shi na tafasa tsantsan bacin rai baiyane akan fuskar'sa wanda shi, kan'shi yarasa ko na menene ga kuma 'yar banza yunwa da yakeji hanji'n Ciki' shi sai faman qugi yakeyi, ya yi wa sigarin wawa zuka ya jefar'da "filter" yakara ciro wata daga cikin kwalinta ya cina mata wuta da "lighter" da ke rike a hannu shi na dama wayarsa tayi "ringing" yaja dan karami'n tsoki sakamako gani "number" Dr kabeer a kasalance yayi "receiving" kb ya akayi"? a bangare daya aka amsa masa da cewa bansaniba wai dan Allah ina ka shiga ne amar"? Ina gida akwai matsala ne"? Uban me ka keyi gida ciki'n mata ga "friends" dinka suna neman ka ko kana nufi ni zan kula maka da su"? Amar yayi murmushi hade da cewa ka fiye korafi kb, ka basu "juice" mai sanyi su sha saboda nasanka da iya "entertainment" din baqi yakarasa magana yana dariya zolaya Mtwww....kabeer yaja tsoki yace nabaka "15 minutes" in baka dawo ba nima zan ware na bar su Dr Michael su cigaba da yiwa daddy gadin, "guest's house" din'shi yana karasa zance'sa ya katsi waya'r. Amar ya tabe baki hade da cewa ka ji da Shi masifafe kawai yacigaba da zukar sigari shi. Horn din akayi shi yajanyo hankali amar ya kalli "gate" da sauri yaciro sigari daga bakinsa ya jefar da ita bala driver ne yashigo yayi "parking" raheela da kawata Zainab suka fito daga ciki'n motar ciki'n yanayi na wanda suka kwaso gajiya su ka nufi cikin gida, amar da ke zaune yana kallon su kawai yatsince kan'shi da kwallawa raheela kira "kee raheela zo nan"! Raheela ta ya mutsa fuska tamkar za ta fashe da kuka, ta kalli zainab tace aiki'n me zan yiwa "guy nan yake mini wannan kira na 'yan farauta"? Zainab tace "oho"! Ki je mana ko menene za ki ji, amma ga dukan alamu, yau rashin mutuncin "hero ya motsa, raheela ta zaro idanu hade da cewa yau fa ranar auren shi ce miye gamin sa da rashin mutunci"?, zainab tayi murmushi tace in banda rashin mutuncin shi ne ya motsa me yakeyi a gidanan"? na shiga uku ka dai duka na za yi, Zainab"? raheela tafada ciki'n yanayi da ke baiyanar da ta tsorata a fili. Keee!" ba magana nake yi da ke ba ko sai kin gama shawara"? Da sauri zainab ta nufi ciki'n gida yayida raheela ta bita da kallo daga bisani dole ta nufi wuri'n amar, daga nesa da shi taja tayi tsaya tace yaa amar gani yayi banza da ita yacigaba da "operating" din wayarsa saida tadauki tsawon 5 minutes" a tsaye batare da ya kalle ta ba a zuciya raheela tace amma "guy" nan cikkake dan wulakanci ne ya za'ayi ka kira ni na zo kuma ka yi banza da ni nima bari na gwada masa nawa kalar' iskanci, ciki'n daga murya tace yaaaaa amar, ganiiii...a tsorace amar ya dago saura kiris wayar a hannu shi, tafadi. Ya waro ido cikin tsananin masifa yace wannan wane irin iskanci ne"? Raheela ta taro baki hade da cewa to ina magana ka kyale ni shine nayi tunani ko "earpiece" ne makale a kunne ka tun da dai nasan kai ba kurma bane Shiru amar yayi yana kallota daga bisani yace arziki ki daya wayar nan bata fadi ba don da tafadi taci "screen" da sai na yi miki duka akawo wuka" raheela takara waro ido tace cabdijam!" akan wannan "china phone" a fusace amar yace uban wa yafada miki "china ce"? A yatsine raheela tace kawata sa'adatu tana da irinta ita tace da ni china" ce kuma tace a jikin'ta a rubuta "made in China" cikin zafin rai amar yace zo ki nuna mini inda aka rubuta "made in China" tabe baki tayi tace da ace sa'adatu tana kusa da na kirata ta nuna maka saboda ni bansaniba amma fa babu shakka wannan waya mai kama da "tray" china ce takarasa magana'rta tana murguda baki. Amar yakara harzuka ya mikawa raheela wayar yace karbi ki kaiwa sa'adatu ta nuna miki inda aka rubuta "made in China" sai ki zo ki nuna min" raheela ta make kafada tace inda gaske ka ke yi ka ajiye wayar bisa mota kayi nesa da ita sannan na zo na dauka yanda wannan fatar tawa, tasha gyara ba zan yarda ka tabata ba. Mtssww...amar ya ja tsoki yace miye abin gyara a wannan fatar taki mai kama da fatar kunkuru, raheela ta murguda baki hade da cewa !"oho" dai, amar ya ajiye wayar bisa mota yace zo kidauka, raheela tace to Kara matsawa mana amar ya galla mata harara yace in za ki zo ki dauka gatanan in kuma za ki tsaya iskanci ki ne "bismillah!" raheela tayi wuf ta dauki wayar saida tayi nisa kadan da shi tace wai dama yaa Amar don ka nuna min wannan "china phone" din yasa ka kira ni"? Ciki'n zafin nama Amar ya je chafko ta ae kuwa ta falla da gudu.... [11:36AM, 5/23/2016] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~4⃣2⃣~ Tashiga gida a "corridor" da ke sada ka da babban falon taci karo da yaya Hafsat tace lah"! Yaya hafsat ina za ki je"? Hafsat ta galla mata harara hade da cewa kina nan yanda nasanki raheela har yanzu ba ki chanza ba, raheela ta kyalkyale da dariya tace hmm..yaya Hafsat wannan gudu da kin ka ga ina yi na ceto rai ne, takarasa zanceta tana yarfe hannaye karaf idanu hafsat su Ka sauka bisa kunshi hannuta, ta riko hannu nata hade da cewa '!iyeee 'yan mata kaka irin wannan kunshi haka sai kace ke ce amarya, raheela ta washe hakora tace na hadu ko yaya hafsat"? Sosai ma kuwa mu ga dayan hannu, raheela ta mayar'da waya a hannuta na dama ta mikawa hafsat hannu'ta na hagu a hankali idanu hafsat ya suka hasko mata dan yatsa raheela tace umhh....'yan mata kaka ina kuma ki ka sami "diamond ring'? Raheela takara kyalkyalewa da dariya tace wane irin "diamond aunty hafsat"? Wannan zobe karfe ne ko don kin ga yana kyalli"? Hafsat ta yi murmushi tace ba karfe bane raheela, zobe ne mai daraja gaske da za ki ji kudi'nsa sai kin girgiza, raheela ta zaro ido hade da cewa kutt..ashe abun kwarai ne yaa Amar yabani Hafsat tace amar kuma amar ne yabaki wannan zobe"? "eh shine har wani cewa ya yi wai zuciyar shi ne, mamaki ne ya lullube hafsat tacigaba da kallon dan yatsa raheela daga bisani tadago tace ae naga alama saboda ga zane zuciya'r ta sa a jikin zobe, har raheela ta yi yunkuri kara tofa albarkaci bakinta ta ji murya zainab tana kwalla mata kira da sauri ta ce yaya hafsat sai kindawo bara nashiga ciki Zainab na jira na, takarasa shigewa falo tabar hafsat da dinbi mamaki. ******************** Da misali karfe 10:00 na dare aka fara gabatar'da "dinner party" angwaye da amare sun sha kyau kowane su makale da amaryar sa bisa "high table" su na'eema an yi wani lafewa jikin Amar yayida fuskar Amar ba yabo ba fallasa, raheela da Zainab suka ratso tsakiyar fili su ka nufa "high table" duk wanda ya kalle raheela sau daya sai kara kallon'ta sakamako tsanani kyau da ta yi sai kace ita ce amarya, tafito da waya'r amar da ke hannuta tafara daukar angwaye da amare "pics har ta eso kan Amar da na'eema don tsabar tsokana irin na raheela, sai tace "wow! Beautiful what's a matching couple's kun yi masifar kyau dole na haskaku da "camera" sabuwar waya'r nan tawa, kallon mamaki Amar yasoma aika mata na'eema kuma tasoma watsa mata harara amma raheela ko a jikin'ta sai ma kara cewa ta yi yaa Amar "smile" kawai tadauke su photo ta kuma mikawa Zainab waya'r ta koma bayan su ta dafa kafadu su tace Zainab haska ni da su kuma ki tabbata ya yi kyau saboda ina so na daura akan "instagram" 'yan uwa da abokan arziki su sa musu albarka, saukar hannuta bisa kafada'r Amar ya hadasa masa shiga ciki'n wani yanayi jin yakeyi wani irin "shocking yana jan sa ya lumshe "sexy eye's" dinsa Zainab ta dauke su raheela ta matsa daf da kunne Amar ta rada masa "thanks 4 d phone" duk lokacin da ka bukaci "sim card" dinka, ka yi min magana har ta juya takara dawowa tace karka ka manta ka aiko min chaja tana karasa zanceta ta juya Amar ya bi ta, da "eye's" wani kololo bakin ciki mai cike da tsantsan kishi ya turnuke na'eema ta nemi yawu bakin'ta tarasa bata kara shiga tashin hankali ba saida ta ga gaba daya hankali Amar yafita daga jikinsa, zuciyar'ta tace tabbas tsugunne bata qare ba akwai sauran rina akaba wannan shi ake kira an kashe maciji ba'a sare kai ba, ta bangare Amar kuma sauke gwaron numfashi yayi sakamako, gani raheela ta bace wa gani sa a zuciya'rsa yace kin zama mahadin rayuwata raheela a duk lokacin da na ganki sai nashiga rudani narasa natsuwa, da kwanciyar hankali'na inda kuma na kusance ki sai naji tsanar ki, jin ya yi a zungure shi a kafa da sauri yadawo da natsuwa'r sa ya kalli na'eema da ta hade rai sai cika take tana batsiwa, ya tabe baki ya kawar'da fuskar'sa da barin kallon'ta abunda yakara harzuka ta kenan a fusace tace kadaina biyewa shaddan yana maka sakar da bata saquwa, domin raheela ta haramta a gareka ko a jahiliya period" ba'a taba hada ya da kanwa ba don haka ka fitarda ita salu-alun daga zuciyar'ka shine kwanciyar hankali'nka tana karasa zanceta ita ma kawar'da fuskarta. Mtwww....Amar ya ja tsoki batare da ya tamka mata ba yacigaba da zance zuci sa, umhh..kenan raheela wayo ta yi mun ta karbe min waya, lallai yarinya nan ba karamar throne" bace yasaki murmushi hade da cewa raheelaaah"sai kuma ya wani lumshe ido. Sai misali karfe 12:30 na dare aka tashi daga "dinner" ****************** WASHE GARI Da misali karfe 4:00 na yamma aka gabatar'da walima, ance ansha sai misali karfe 6:12 aka tashi daga walima, raheela da Zainab sun rako wasu kawaye su a bakin "gate" ya yi dai-dai da lokacin da Amar yadanno hanci motar'sa da sauri raheela tace da kawaye ta sai anjima ku na gode sosai ku gaida gida nufi'nta ta arci na kare bataso Amar ya ganta saboda tun jiya rabo ta da tasaka shi a ido, sakamako tana jin tsoro haduwa da shi domin tasan masifar da haduwar tasu za ta janyo mata tattara siket din'ta tayi ta kwasa da gudu ta shige part din kaka. Amar yafito daga ciki'n mota ya bita da kallo domin yasan saboda shi take wannan gudu, a falo Zainab tarar'da ita tana haki zainab ta kyalkyale da dariya tace ni ina ganin 'yan fashi da makami bantaba gani irinki ba raheela haka kawai ki yiwa bawan Allah fashi waya, raheela tasauke ajiyar zuciya hade da cewa laifi sa ne duk lokaci da ya kyalla ido ya ganni da waya sai karbe yace wai sai na kamalla "secondary school" zan rika waya ko ina ruwa'nshi da ni !oho. Zainab tace Allah sarki my real hero" yana ji da ke raheela, tamkar tsoka daya a miya, raheela ta yatsine fuska tace kyaji da shi. Da daddare misali karfe 8:30 aka kai amare gidanje angwaye su, kowane su ka shiga gida'nsa bakaso fitowa saboda tsananin haduwa da gidanje su ka yi anci mutuncin naira, kamar baza'a mutu ba. Na'eema da kawaye ta zaune suna jira zuwan ango da abokanai sa har 10:30 ta buga, ba Amar ba abokai sa, dole kawaye na'eema su ka yi ta kansu ran na'eema ya yi matukar baci ta kifa kai bisa "pillow" tana shashekar kuka me Amar yake nufi da wannan wulakanci da ya tafka mata'? Abunda na'eema bansaniba tun misali karfe 9:00 Amar yake ciki'n gidan ta kofar baya ya bi yashige "part" din'shi, ya yi wanka yasaka "pajamas" blue colour" jikinsa na fitar'da kamshi turare "designer" sumar kanshi na kyalli ya nufi falon ya kunna tv yana kallon ga kwali'n sigari sa bisa "stool" sai faman zuka yakeyi da takare yakara kunna wata, duk lokacin da rufe idanu sa raheela yake gani, ya cilla "filter" cikin ash tray" yakara zaro wata yacina mata wuta, da sauri yajuya bakin kofa sakamako kamshi turare "violet rose" da yadaki hanci sa na'eema yagani tsaye cikin wata shu'umar night gown" ita da babu duk daya ya tsura mata idanu yana kare mata, kallo ya tsayarda idanu sa bisa kirjinta da ke baiyane, ya hadiye yawu, dama ga Amar da tsananin sha'awa nan take idanu gogan naku su ka, kada su ka yi jajir, sai kawai ya kawarda idanu shi da barin kallon'ta, ciki'n tako na yanga na'eema takaraso kusa da shi ta zaune, jikin'ta na gogar nasa hannu shi, tariko cikin kissa da kisisina ta yi kasa da murya tace yaa Amar yaushe kafara shan sigari"? Amar ya yi shiru sakamako yanda take shafar hannu shi tuni yafada tarko ta, janyo ta ya yi tafado bisa jikinsa yasoma sunbatar'ta yayida na'eema take mayar mishi da martani yadauke ta chak ya nufi "bedroom da ita da kyar su ka iya yin nafila raka'a biyu sai kace wasu mayu su ka fara "romance" din juna Amar ya kashe wuta bakaji komai sai sauti kukan na'eema yayida Amar bai fasa abunda yake yi ba sai ma yafara zazzaga mata surutu mai cike da rudani surutu da ya yi sanadi rushe duk wani farin ciki jin dadi ta, "I love you raheela you are so Swéet you are d star dat makes me shine, your love is d most precious gift I have ever had I really love's you raheela. Na'eema batasan lokacin ta kurma ihu da ya yi sanadi da Amar yadawo haiyyaci shi ciki'n shashekar kuka tace "first night" dinmu na kawo maka budurci na yaa Amar amma kadinga kira na da suna raheela wannan wane irin wulakanci ne"? Sai lokacin "brain" dinshi yafara yi masa "backwards din abunda yafada sai kawai ya yi tsuru-tsuru alamu rashin gaskiya su ka baiyana akan fuskar'sa gani yanda na'eema take kuka tamkar ranta zai fita yasa Kara matsi ta a jikinsa yace I'm sorry na'eema please forget & forgive me" dazu da yamma raheela ta bata min rai abun ya tsaya min a zuciya sosai wannan baci ran ne, na tuna da shi datz why na kira ki da sunanta amma wallahi babu abunda ke tsakanina da ita ke kan'ki sheda ce akan irin tsanarda na yi mata. A fusace na'eema tadago jajaye idanuta tace....... Jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:37 am] Jeeddah Aliyu🌹: [11:05AM, 5/26/2016] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~4⃣3⃣~ A fusace na'eema tadago jajaye idanuta tace ba wani tsana'rta da ka yi kadai har yanzu sonta yana nan makale a zuciya'rka, to kasani raheela tariga ta haramta agare ka, mafi al'khairi a tare da kai shine fitarda ita daga zuciyar'ka domin har abada bazaka taba samu ta b...da sauri amar ya katsita, ta hanyar hade bakin'sa da nata yacigaba da tsotsi "lips din'ta yayida na'eema ta yi wani lafewa gani yana kokarin tsalka "border" yasa tafashe da kuka cikin murya shagwaba tace yaa Amar nagaji dan Allah ka kyale ni haka bakaji yanda jikina yake min tsami ba, Amar ya shafi fuskar'ta hade da cewa kedai raguwa ce, turo baki ta yi tace "Eh na ji din ni ruguwa tun da na kawo maka kaina har "bedroom" dinka za ka iya kira na da kowane irin suna takarasa magana'rta tana kokari mikewa tsaye, da karfi yajanyo ta tafada bisa jikinsa ya matsi ta sosai yace yaushe ki ka koyi korafi na'eema"? Ta galla masa harara hade da cewa "oho nima bansaniba, karan hancin'ta yaja yace bara naje na hada miki ruwan wanka, batare da yajira jin ta bakinta ba ya mike yanufi "bathroom" bayan sun yi wanka tana kwance bisa kirjin'shi yana shafar gashi'n kan'ta kamar, daga sama ta ji sautin zazzaqa muryar sa yana fadar ya akayi "my na'eema, raheela tafi ki gashi"? A harzuke na'eema tace gashi kadai za ta nuna mini badai kyankyawan asali ba sannan kuma kowa yasan raheela sadaka yalla ce batada cikkake asali, takarasa zanceta tana huci. Amar ya waro idanu yace maida wuka 'yar uwa daga magana, sai ki haye kamar farashi man fetur, kuma da ki ke zance raheela batada asali kenan nima banida asali domin abunda ya yi raheela Shi ya yi ni karki manta da mahaifiya ta da mahaifiyar raheela ciki daya su ka fito. Dakata yaa Amar don girman Allah ka kyale zuciyata ta huta da zance, raheela wai me raheela ta mallaka maka da ni ba zan iya mallaka maka shi"? Amar yace "Allah ya huce zuciyar'ki my na'eema ban yi nufi na bata miki rai ba amma ki yi hankuri ba zan kara kiran sunan raheela. Na'eema ta narke bisa kirjinshi tana sharar hawaye, yayida shi kuma yacigaba da rarrashinta hade da kalamai masu dadi gaske a haka bacci ya yi awo gaba da su. WASHE GARI******** Tun da asuba da Amar ya falka ya je masallaci bai bi ta kan amarya na'eema ba ya koma bacci, abin shi na'eem nagani haka ta ja sanyayu kafafu'ta ta fice daga daki'n, har karfe 10:30am ta buga Amar yana sharar bacci, na'eema ta ke zaune falo tana jira fitowar Amar ta ja dan karami'n tsoki hade da Mikewa tsaye a zuciyata tace wannan wane irin bacci ne"? Ni fa yunwa nakeji wannan bawa Allah ko ya manta cewa ni amarya ce ina bukatar tattali da kulawa na musanman daga gare shi, kaitsaye ta danna kai ciki'n "bedroom" din'shi yana kwance bisa makeke gadon shi kirar "royal bed" ga wani bedsheets mai tsananin laushi gaske rabi jikin shi, na rufe da "blanket" sanyi "air conditional" yana ratsa shi, chak na'eema ta ja tayi tsaye ta kuma zaro idanu ta, sakamako sautin murya Amar da ke ji yana kiran sunan raheela wanda hakan ya tabbatar mata da mafalki ne ya keyi raheela" raheela ina tsanani son'ki bana tunani zan rayu batare da ke ba ki amince da ni na nuna miki tsantsan son da na ke miki zan iya sadaukar da komai nawa domin na same ki, ki tausayi, Mini raheela ki mallaka min kan'ki ni kuma nayi miki alqawali zan zama tamkar bawa agare ki. Na'eema kan mutuwar tsaye tayi hawaye su ka wanke mata fuska nan take tafara nadama abunda ta aikata bata ga amfani wannan asiri da ta yiwa Amar domin bai raba shi, da son raheela ba yayida Amar yacigaba da tsoki burutsu shi gani abun yafara wuce minsali yasa takarasa wurin shi ta tattaro karfin'ta waje daya ta narka masa wawa duka a ciki, a razane Amar ya mike zaune, na'eema na tsaye tana aika masa mugun kallo, ciki'n tsanani mamaki ya bude baki yace keee! Kan'ki daya wannan wane irin iskanci ne haka aka koya miki tayarda miji daga bacci"? Mtwww...na'eema ta ja tsoki ciki'n tsantsan takaici'n tace wai me ka ke nufi da ni yaa Amar"?karka manta raheela kanwa tace aure ya haramta a tsakani ku, ka taimake ni kafitarda da ita daga ranka, ko zan sami kwanciyar hankali nima na more rayuwar aure, batare da Amar ya furta uffan ba ya sauko daga bisa gado ya nufi "bathroom yabar na'eema tsaye tana kuka, gani kuka ba zai zame mata mafita yasa ta kwasa da gudu nufi, dakin'ta. Amar yana wanka yana tuna mafalki da ya yi nan take wata shaharariya kunya ta lullube shi, yasoma tunani da wance kalma zai yi amfani da ita waje ba na'eema hankuri tabbas yasan yana tsanani son na'eema, amma yarasa dalilin da yasa yakasa cire raheela daga ranshi duk lokacin da ya ganta sai ya ji wata sabuwar tsanar'ta tana kwarara a zuciya'rsa inda kuma yakadai ta sai ya ji wata sabuwar soyayya'r ta tana linkaya a cikin kashi da jijiyo jikinsa, a wasu lukuta ya kanji tamkar ba zai iya cigaba da numfashi batare da ita, wannan wace irin masifa ce Amar yafada a baiyane yakasha "shower yafito daga "bathroom" ciki'n sauri yasaka kayan shi yafito yana sanda kamar barawo, na'eema da ke tsaye a bakin kofar dakin'ta tace kai da gidan ka miye na sanda"? Amar ya tsaya chak, sai faman muzurai ya ke yi na rashin gaskiya, har na'eema takaraso waje shi yana nan tsaye kamar bishiyar kwakwa ta riko hannu shi ciki'n sanyi murya tace mu je ka yi "breakfast" har Amar ya yi yunkuri bata hankuri ta dakatar da shi, ta hanyar cewa banaso jin komai daga bakin'ka yaa Amar domin hakan zai iya kara jefa zuciyata cikin 'kunci da takaici don haka ka adana kalaman ka saboda a halin yanzu ba za su iya sanyaya mini zuciya kawai mu je kayi "breakfast" Ba yanda Amar ya iya dole ya hadiye 'yan kalman sa ya bi bayan ta wance tuni ta tsofa a dining area" ta ja masa kujera ya zauna sannan ta hada masa "tea ta kuma zuba masa chips" ta tura masa a gabanshi, duk da yana jin yunwa kasa sakewa ya yi ya ci abinci, yayida na'eema sai bishi da kallo ta keyi, gani ya mike yasa ita ma ta mike, ta mara masa baya a tsakiyar falon ya ja ya yi tsaye ya tattaro natsuwa da jarumta shi yace na'eema ni zan fita ko kina da bukatar wani abu ne"? Ta girgiza kai gani taki yi masa, magana yasa karaso daf da ita yafisgo ta da karfi tafada kirjinshi yasoma rada mata kalamai masu dadi gaske sai ga na'eema ta watsake har da su kyalkyala da dariya yadago fuskarta yasake mata dafi "kiss a lips" yace sai nadawo my na'eema, saida ta wani lumshe idanu daga bisani ta bude su tace adawo lafiya yaya naa, ya juya yafice daga falon tabishi da kallon kauna. Amar yana fita yanufi gida sakamako zuciya'rshi da ke azalzala shi da son gani raheela yadanna horn maigadi yabude masa gate yayi parking daga bisani yanufi "part din kaka... [6:43PM, 5/26/2016] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~4⃣4⃣~ Da sallama yashiga falon saidai falon tsit yake ba kowa a ciki, kaitsaye yadoshi "bedroom" din kaka hannaye shi na zube ciki'n aljihu wando shi, ya murda handling" yashiga cikin daki hango ta ya yi kwance bisa gadon kaka tana rungume da pillow" tana sharar baccinta ciki'n kwanciyar hankali da gani yanayi ta batada matsala, a hankali yake tafiya har yakaraso kusa da ita ya tsura mata idanu, yayida zuciyar'shi ke bugawa da sauri-sauri tamkar za ta faso kirjinshi ta yi tsalle tafado kasa ya cigaba kallon kyakyawa fuskar'ta wance yakasa banbance tsakani tana bacci da tana falke wane tafi kyau yakara mayar'da gani shi, akan pillow da ta yiwa kyakyawar runguma a zuciya'rshi yace ina ma ace ni ne ki ka rungume raheela ba wannan dan banza pillow mai tauri tsiya, yakara yada gani shi akan "pink lips" din'ta wanda duk lokacin da ya kwanta bacci sai ya yi mafalki ya sumbace su nan take ya kudiri anniya sai yadan lasa su ko zai rage jin radadi da zogin da zuciya'rshi ta keyi masa akan wannan taurarowa da ta mayar da rayuwar shi tamkar ball a raga, batare da wani dogon tunani illah da hakan za ta jefa shi ba ya zauna kusa da kan'ta ya sunkuya dai-dai bakin'ta ya sumbace ta, raheela kan bacci'nta takeyi batasan waina da Amar yake toyawa a hankali yazare "pillow daga kirjin raheela saboda wani irin zazzafan kishi pillow yakama shi gani yakeyi pillow baidace da yasami mutsugunni a kirjin raheela ba, yariko hannuta ya tsurawa kunshi hannuta ido a hankali yake shafar zane kunshi da dan yatsa shi, a ciki bacci raheela ta ji ana mata tafiyar tsotsa a hannu'ta a firgice ta falka tana bude idanu taci karo da fuskar Amar yana zaune rike da hannu'ta da sauri ta fisge hannu nata ta tashi zaune tana zarar idanu, yayida Amar yacigaba da kallon'ta ciki'n sarkewa halshe tace dan Allah yaa Amar ka yi hankuri, dama ina da niyar baka wayar k.....saura kalman ta suka kargame a makoshi'nta sakamako dan yatsa shi da yadaura akan "lips din'ta yace shhhhh..tsawon dakika uku zuwa hudu su ka dauka suna kallon juna daga bisani Amar ya murtuke fuska yace ina waya ta"? Gaba daya raheela tagama tsorata babban tashin hankali'nta bai wuce kaka tayi samako ta tafi gaisuwa rasuwa 'yar aminiyar ta da rasu ballatana ta kwace ta hannu Amar, yau na shiga uku abunda raheela tafada a baiyane, Amar ya yi murmushi, hade da cewa baki shiga uku ba da saura don sai kin nuna min inda aka rubuta "made in China" a phone dina. raheela takara zaro dara-dara idanuta masu cike da tsoro ta kuma kwabe fuska kamar za ta fashe da kuka tace, Allah yaa Amar karya na ke yi banida qawar da take da irin phone dinka da sauri tadaga pillow tadauka waya ta mika masa, yagame wayar da hannu'ta yarike ya kalle dan yatsa ta da ke makale da zobe da yabata, yace ashe baby har yanzu zuciyata tana nan tare da ke"? Raheela ta wangale hakora tace cab yaa Amar ae in har ka ga zobe nan yabar dan yatsana to bana numfashi, Amar ya zaro ido, raheela tacigaba da cewa tun ranar'da yaya hafsat ta gayamin diamon" ne nake tattali shi kamar tsoka daya a miya ta karasa magana tana dariya. Amar ya dan murmusa, yace ke kan'ki "diamon ce baby dama kan'ki ki ka dinga yi min tattali ba wannan zobe ba, tabe baki ta yi hade da cewa 'hmm. Amar yasaki hannu ta ya balle murfi wayar ya Zare sim card din shi ya rufe wayar ya mika mata yace ga wayar nan na barki miki ba don halin'ki ba in nadawo anjima zan kawo miki "SIM" cikin zumudi raheela ta karbe wayar tasoma zuba masa godiya, ya mike tsaye yace ina wannan masifafiya tsohuwa ne banji motsin ta ba tun lokacin da nashigo? Raheela tayi murmushi hade da cewa tafita unguwa, Amar Ya tabe baki yace gaske dai naci kare na babu banbaka da tana nan da yanzu ta hanani rawar gaban hantsi, a wannan karo raheela batace da shi komai kawai tacigaba da jujuya wayar hannu'ta fuskar'ta na fitar'da annuri farin ciki gani ta shagala da kallon waya yasa yafice daga daki'n yanufi 'part din mamee. ********************* Tabangare amarya na'eema kuma bata kara saka angonta a ido ba sai da yamma lis yadawo tana zaune falon taci kwalliya tana zuba ido ta ga inda angon nata zai bullo. Amar ya yi sallama yashigo falon da sauri na'eema ta mike tanufi shi ta fada kirjin shi ya dan rungume ta yana shafar bayan ta yace my na'eema ya zama kadaci yaa yatafi yabarki koh"?? A shagwabe na'eema tace har da kuka na yi, Amar ya yi murmushi yace kinfiye shagwaba na'eema, miye kuma abun kuka sai kace na bata"?, takara narkewa bisa kirjin'shi tace to ba kai bane tun safe da kafita baka dawo ba sai yanzu, Amar yakara saki dan bazawari murmushi yace to sakeni na je nayi wanka lokacin sallah magarib yakaraso. Ciki'n hanzari tasake shi tace mu je na hada maka ruwan wanka, tawuce gaba Amar ya mara mata baya kaitsaye ta wuce 'bathroom ta hada mishi ruwan wanka koda tafito tarar'da shi yatube daga shi, Sai boxers da sauri tarufe fuskarta ya tabe baki ya bi ta gefe ta yashige "bathroom na'eema ta bude fuskar'ta tafice daga daki'n zuciya ta cike tsantsan son Amar. Amar yana fitowa daga wanka yanufi "dressing mirror yadauki body lotions ya shafe jikin shi yakara daukar "comb ya shace sumar kan'shi, jin anfara kiran sallah da sauri yanufi wardrobe yaciro blue jeans hade da body hook" brown colour ya feshe jikin shi da turare "pure blue" yafice daga dakin gani na'eema bata ciki'n falon kaitsaye yanufi bedroom din'ta karo na farko da shiga daki'n nata, tana zaune a gefe gado ta rafka dan uban tagumi ko tunani me ta ke yi ne oho" batare da damu da yanayi da take ciki ba yace na'eema na tafi masallaci ke ma kitashi kiyi sallah, ciki'n sanyi murya tace toh adawo lafiya, yadaga mata kai yafita daga daki'n. Kaitsaye yanufi parking space ya ja motar'shi yafice daga gidan saida ya yi sallah magariba da esha'e sannan yanufi inda zai je a baki titi ya tsaya wani shago siyarda katin waya yasiyawa raheela sim ya kuma yi mata "register' kara yiwa motar'shi key ya halba kan titi yayida zuciya'rshi tafara yi masa sake-sake shin me ke shirin faruwa da ni"?ada zuciyata raheela take so kwantsan na waye gari cikin so da kauna na'eema, nake kuma jin inda har ban aure na'eema zan iya daina numfashi yanzu kuma na aure ta amma gaba daya zuciyata takarkata akan raheela, wani abin takaici' duk lokacin da nayi arba da fuskar'ta sai naji na tsane ta, wani bangare na zuciyar'shi yace amma kuma dazu ka yi namiji kokari ta hanyar danne kiyayya da ka ke yi mata wanda sanadi hakan ne yajanyo maka farin ciki maras misaltuwa musanman in ka tuna cewa yau ka sumbace tautausan labba raheela, sai kawai ya lumshe idanu shi ya Kuma bude su yakara dankarawa mota giya zuciya'rshi cike da buri'n kara son gani raheela...... Jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:37 am] Jeeddah Aliyu🌹: [2:11PM, 5/28/2016] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕Love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~4⃣5⃣~ Tun kafin yayi parking ya hango raheela da nazeer tsaye a "compound" ko me nazeer yake fada mata take faman kyalkyale dariya nan take ya ji wani masifafe kishi ya turnuke shi, kasa fitowa ya yi daga ciki'n mota ya tsura musu na mujiya yana kallon su. Nazeer ya katsiwa raheela dariya da takeyi ta hanyar cewa ga "big bros chan watakila godiya ya zo ya yiwa umma na 'yarta da mallaka masa ae kuwa raheela takara kyalkyalewa da dariya nazeer ya mike mata hannu su ka tafa, da sauri Amar ya rintsi idanu shi, sakamako wani kololo da ya tokare masa makoshi, Ringing" din wayar nazeer ce ta katsi musu dariya da su ke yi, yafito da wayar daga aljihu rigar shi ya zaro ido yace tawan zan tafi gida amarya ta taso ganina, raheela ta tabe baki hade da cewa su amarya manya da bamusan asali ugulu ba da tace daga kasar masar tafito, nazeer ya yi murmushi yace duk wannan zaurance naki na fahimce inda ya dosa kina jin haushi bahijja ta yi miki "snatching" dina. Mtwww..raheela taja dogon tsoki daga bisani tace ina kuda balle romonsa ae ni bahijja taimako na ta yi tarabani da jangwan dama kaka tace ba mudace da juna ba shiyasa kana furta bahijja ka ke so nima son'ka yafita daga zuciyata sai daga baya nagano cewa shakuwa ce a tsakani mu ba so ba takarasa zanceta tana dariya. Nazee yabata fuska musanman da ya hango gaskiya abunda raheela tafada cikin kwayar ido ta ciki'n sanyi murya yace sai anjima raheela saboda nafara gajiya da wadanan munana kalaman naki, raheela tace saidai da safe domin na tabbata in har ka shiga gida bahijja ba za ta kara bari kafito shikenan yaya nazee ka zama mijin tace a fusace nazee ya kai mata duka ta goce bai same ta, tabangare Amar kuwa ji yake yi kamar ya balle murfi Mota ya fito yahade nazeer da raheela ya yi musu shegen duka, nazee ya kalli raheela da ke nesa da shi tana masa dariya ya galla mata harara yajuya yanufi "parking space" Amar yana gani nazee yadoso inda yake sai yakara murtuke fuska kamar tsoho soja sai faman hura hanci yakeyi, Nazee yakaraso ya leka ciki'n motar yace akayi ne bross"? Sai da Amar yagama shan kamshi sa, a dakile yace ina son gani wance yarinyar ne yanuna raheela da baki, nazee ya yi murmushi hade da cewa okey bara na kira maka ita batare da yajira jin ta bakin Amar ba, ya daga murya Da karfi ya kwadawa raheela kira wance sauri kiris tashige part din kaka kee! raheela ki zo yaa Amar yana kiranki raheela ta tsaya chak daga bisani ta nufi parking space" Nazee yace bross ni zan ware da kyar Amar ya iya bude baki yace ka gaida gida domin jin yakeyi kamar ya shako kwalar rigar, Nazee yace banaso nakara gani ka tare da raheela domin tawa ce ni kadai sai dai kash ba zai iya ba Nazee yace gida zai ji yajuya yashige motar'shi yafice daga gidan. hakan ne yaba Amar damar kifa kan'shi bisa sitari yasoma tunani wannan masifar da yake yunkuri afkawa ciki domin ko a gari shegu bai taba gani an hada ya da kanwa ba, wannan shi ake kira gaba kura baya siyaki, raheela takaraso tadafa murfi mota tace ina wuni yaa Amar" Firgigit ya yi yadago sexy eye's din'shi ya kalle ta kawar'da fuska cikin sanyayar muryar shi yace lafiya qalau" Ina phone din naki nasaka miki sim"? Cikin zumudi hade da rawar jiki raheela ta tura hannu'ta ciki zani ta tafito da wayar ta miqawa Amar'' Zaro idanu ya yi yace kee har yanzu baki daina wannan shashanci naki na boye abun ciki'n "pant wai yaushe za Ki yi hankali raheela"? Raheela tarufe fuskarta da tafuka hannaye ta ciki'n tsanani jin kunya, tace kai yaa Amar dan Allah kidinga tauna magana kafin kafade ta. Amar ya yatsine fuska yace naki na tauna din ae hali'n ki ne nafada ba zan iya tunani adadi yaran da ki ka yiwa kwace kina boye, cikin pants" dinki. Raheela tayi narai-narai da idanu kamar za ta fashe da kuka tace abunda yawuce yaa Amar kadaina tadashi wannan abun da ka ke fada tun na yarinta ne kuma ae cikin zani na ne nasakade wayar. Ya mika mata waya yace ni dai karbi wayarki banaso dogon surutu kuma ina gargadi ki da karki sake ki bawa kowane gardi number ki duk ranar'da nayi checking" din contact naki naga number gardi sai nafasa waya'r nan na kuma kar'ya miki hannu. Cikin sanyi jiki raheela ta mika hannu ta karbi wayar tace na gode yaa Amar Allah yasaka da alkhairi" Amar yace bana bukatar godiyar ki kawai ki kiyaye umarni da na baki. Raheela taro baki hade da cewa ni me zai hadani da number gardi"? Harara ya galla mata yace dan banza rawa kan'ki ne zai hadaki da number" in kuma hakan tafaru kinsan abinda zai biyo baya, har raheela ta bude baki za tayi magana yadaga mata hannu hade da cewa oya shiga gida banaso surutu, har raheela tajuya ta yi tako biyu zuwa uku taja tayi tsaye ta mayar'da ganinta waje Amar tace yaa Amar baka saka min number ka ba"? Amar ya yi dan bazawari murmushi yace zan kira ki sai ki yi serving tace toh..na gode ka gaida yaya na'eema ta juya tashige bangare kaka. Amar yaja mota yanufi gidan'shi zuciya'rshi cike da dinbi tunani yakamata nadaina yaudara kaina nagano cewa raheela ta yi min nisa, ba zan taba samunta ba, dole na hankura da ke raheela don haka mafi alkhairi a tare da ni in tattara komaitsa na koma abuja watakila in na nisance ki zuciyata ta rungume kaddara, da wannan tunani ya esa gidan'shi. A falon yatarar'da ita tasha ado ciki'n wasu hadadu sleeping dress" riga da wando fuskar'ta shinfide da damuwa, tana gani yashigo tasauke ajiyar zuciya tace sannu da zuwa" Yauwa" iya abunda yafada kenan yanufi bedroom dinshi da sauri na'eema ta mara masa baya kaitsaye yanufi toilet ya yi wanka yana fitowa ya ci karo da ita zaune a gefen gado, yabude wardrobe yaciro pajamas yasaka yafashe jikin shi da turare "suphoria men" ya haye gado ya yi kwanciya shi na'eema tace yaa Amar ba ka ci abinci ba kuma naga ka kwanta, Amar yace na koshi na'eema in kina ji bacci ki zo ki kwanta, ba yanda na'eema ta iya dole ta raba gefen shi ta kwanta, kowane su ya yi shiru yana tunani daga bisani na'eema ta yi namiji kokari, ta rungumo bayan Amar tasoma shaqar Qamshi shi, cikin zafin rai da daga murya sai kace commander" sojoji Amar yace stop it's na'eema I don't want's any disturb right now so leave me alone" A tsorace na'eema take kallon shi hawaye na kwarara akan fuskar'ta cikin shashekar kuka da ke baiyanar da bakin ciki da takaici tace nashiga uku ni na'eema wannan wane irin tasko ne nake gani, tsakani jiya da yau naga wulakanci maras adadi daga gareka yaa Amar, kuma nasan kana wulakanta ni ne duk saboda raheela to kasani yaa Amar, yanda Annabi ya haramta da wuta haka kaima ka haramta da raheela, kuma na kudurci aniya sai na ja dogon layi mai tsayin gaske tsakaninka da raheela koda hakan zai kasance bugun numfashi na a duniya tana karasa zanceta tafice da gudu Daga daki'n. Amar yaja tsoki yace kan'ki akeji mahaukaciya banza jarababiya haka kawai za ta hanani bacci ya gyara pillow ya yi kwanciyar shi. ********************** WASHE GARI**** Da misali karfe 8:30am Amar yafito daga dakin'shi yasha kwalliya cikin wata dakakiya shadda galila dark blue colour" wance tafito da sahirtace kyaun shi sumar kan'shi tasha gyara tayi luf-luf da ita sai kyalli ta ke yi ga wani uban Qamshi da yake zubawa, yafito ango sak amma kuma ango da bai da moriya cikin tako sa na kasaita yanufi falo yayida na'eema da ke zaune tadago ta kalli shi take tsananin soshi yakara mamaye zuciyar'ta batasan lokacin da tace ina kwana yaya"? Kallon kasan ido yayi mata wanda hakan yakara jefa ta ciki'n wani yanayi yace lafiya qalau ki je ki hada kayanki za mu tafi abuja yanzu nan. Na'eema ta zaro ido tace lafiya kuwa yaa Amar"? Kinga malama in kina da ra'ayi zuwa ki je ki hado kayan'ki da sauri na'eema ta mike tanufi ciki'n dakin'ta..... [9:37PM, 5/28/2016] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~4⃣6⃣~ Ko da tafito yafice daga falon hakan ya tabbatar Mata da yafita dole ta rufe kofufi gidan, daga bisani ta ja katuwar "trolley" dinta ta nufi compound din gidan a parking space" ta tsinkaye shi tsaye takarasa waje shi, ya karbi "trolley ya jefa a seat din baya yajuya ya zauna a "driver seat" yayida na'eema kuma take zaune a gefen shi, ya yi addu'a ya ja mota ya tsaya bakin "gate ya yi sallama da maigadi sannan yakarasa ficewa daga gidan. ********************* Raheela ta fito daga daki hannu'ta rike da jakkar littafai ta na islamiyya tashigo falo ta kalli kaka da ke zaune da casbaha hannu tace kaka zan tafi isalamiyya. kaka tadago ta kalle ta, tace "oh Allah gagara misali wai raheela yaushe za ki natsu ne"? Raheela ta turo baki Ciki'n shagwaba tace me nayi"? Kaka tace ba kiyi karin kumallo ba kin dauke duniya bisa tsinke kina tsotsa ni narasa munafuki da yasiya miki kattan na duniya bisa tsinke nan baki da aiki sai na tsotsi-tsotsi duk inda ki ka ga dama sai ki jefar min da tsinke, ke ko tsoro bakyaji kada basir yakama ki ga kuma wannan munafuka waya da wannan gantalale yaro yabaki nace ki mayar masa da tsiyar sa amma ki kayi kunne uwar shegu da ni. Har kaka ta dasa aya a zanceta raheela tana Kallon ta, daga bisani tafara magana kamar za tayi kuka haba! Kaka wannan fada duk akan waya ne"? To ni dai gaskiya Saidai ki yi hankuri ina son waya ta takarasa magana tana murguda baki. Kaka tace shikenan tun ke ba'a fada miki ki ji ae sai ki tayi, indai Amar ne ina nan zan ji labari ta matsi muku. Raheela tayi murmushi tace kaka kenan mugun fata da ki keyi mana kenan"? To insha Allah ba za ta matsi mana ba. Umhh...Allah yasa domin Amar shu'umi ne na karshe, ko uwar da ta haife shi bata gane inda yadosa ballatana ke karan kada miya. Oh! Ni raheela kaka ba dai korafi da sa eye's ba na fahimci tun daga ranar'da yaa Amar ya yi miki PDP ki daura mishi karan tsana takarasa zanceta tana dariya. Ae kuwa kaka takara harzuka tace ya dai yiwa kan'shi PDP domin na tabbata indai rai da rabo wata rana za ta bare mishi da kan'shi, zai nemi ni. Toh...ae shikenan sai ki jira in zo sai kifada masa ni miye nawa a ciki"? Akwai domin ke ce mai kunne qashi da ki ke kula shi, raheela ta zaro ido hade da cewa cab yau tsohuwa nan masifa safe ta keji sai ki jira mai tsautsayi da zai fado falonki, sai ki wanke masa allo shi son ranki, ni kan kinga tafiya ta, tajuya tafice daga falon cikin daga murya kaka tace ki tabbata kin cire tsinke nan daga bakin ki kafin kifita gidanan. Raheela tace kullum haka ki ke fada, sai kace an gaya miki da shi nake fita. Kaitsaye part din iyayye ta ta nufa, a dining area tarar'da su zaune bisa dining table" ta runsuna ta gaida abban taa tajuya ta gaida aunty amarya, yayida ko kallo umma hajara bata esheta ba, ta nufi kujera da alhaji Abdullah yake zaune, aunty amarya tadaka mata tsawa cikin bacin rai tace, kan'ki daya kuwa raheela baki ga hajara bane da ba za ki gaida ta"? Raheela ta turo baki kamar za tayi kuka tajuya waje umma tace yakike"? A harzuke umma hajara tace ni za ki kalla raheela ki ce da ni ya nake don tsabar rashin tarbiya, su iyayye ki ae ba haka ki ka gaida su ko don ni kin rena ni. Aunty amarya ta gallawa raheela harara tace ki gaida ta ko na kwada miki mari gani yanda aunty amarya ta zaburo mata yasa ta boye bayan Abba, yayida abba abinci shi kawai yake ci tamkar bai ga abunda yake faruwa ba, hannu shi yasa yajanyo raheela yace zauna kiyi breakfast mama naa, raheela ta bata fuska tace sai nadawo daga islamiyya zan ci Abba. Aunty amarya tace amma alhaji yakamata kadinga tsawatawa maama akan irin wannan rashin kunya da takeyi. Alhaji Abdullah ya ajiye fork din da ke hannu shi yace duk abunda maama ta ke yiwa hajara bana gani laifi ta saboda hajara ce tafara nuna mata baiyananiya kiyayya sai kace da ita ta ke kishi a yanda na fahimce hajara kiyayya da take nunawa maama, ko ke da ki ke matsayin na kishiya ta bata nuna miki irin ta me maama ta tare mata ne"? Umma hajara tace raheela bata esa ta tare mini komai a gidanan, ita da babu duk daya suke a wuri'na takarsa zanceta tana huci. alhaji Abdullah ya yi murmushi ya kalle raheela cikin kulawa yace tashi ki tafi isalamiyya mama na kada kiyi latti hasada ga mai rabo taki, raheela ta mike tsaye taciro waya daga aljihu wando uniform din'ta ta mikewa abba tace abba kalli waya na da yaa Amar yabani, saura kiris umma hajara ta hadiye fork din hannu'ta ta zaro turu-turu idanuta da suka baiyanar da tsanani tashin hankali da ta afka ciki kamar daga sama ta ji murya abba yana cewa iyee lallai yaa Amar ya burge ki mama irin wannan waya mai tsada haka cikin zumudi raheela tace abba ya sunanta ne"?abba yace iPhone6 ce raheela ta daka tsalle ciki'n jin dadi tace abba nima na karo wulakanci kenan"? Abba ya yi dariya yace sosai ma kuwa, raheela tace abba ka yi "checking din account balance dina abba ya yi yanda raheela ta umurce shi yakara sakin dariya hade da cewa "ten thousand" nagani" raheela takara wangale baki tace yaa Amar ne yasaka min abba kayi min serving number ka, abba yana murmushi ya yi mata serving din number ya kuma mika mata wayar. Tun lokacin da raheela ta anbace sunan Amar umma hajara tashiga tashin hankali maras misaltuwa a yanda boka duguzuu yace da su da zarar asiri yakama Amar zai tsani raheela hatta kashi sai yafita daraja da kima a waje shi, amma kuma gashi raheela ta zo da wani sabon bidi'a wai Amar yabata waya lallai ya zame mini dole na koma waje boka duguzuu, murya raheela ce ta katsi mata tunani, da takeyi abba na tafi, yayida umma hajara ta bi raheela da mugun kallo, kamar wance aka cewa tajuyo raheela tajuya, karaf idanu ta su ka hango mata kallon tsana da umma take mata, raheela ta yi murmushi hade da yi mata gwalo, domin duk duniya ba abunda umma hajara ta tsana irin raheela ta yi mata gwalo abun yana kona mata rai da za ta sami sarari, da ba abunda zai hanata gutsirewa raheela halshe. Fitowar raheela daga ciki'n gida yayi dai-dai da parking din motar Amar tun daga nesa ya hango ta numfashi'n sa yafara kai da kawo, na'eema kuma ta murtuke fuska tamkar wance ta hango wani bala'e yana tunkaro ta, cikin wannan yanayi su ka fito daga ciki'n mota raheela, na hango Amar da na'eema takara fadada murmushi'nta..... Jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:37 am] Jeeddah Aliyu🌹: [12:51PM, 5/31/2016] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~4⃣7⃣~ Amar ya ja ya tsaya a gaban'ta fuskar'shi a sake yace 'yan mata kaka'' Raheela tace ina kwana yaa Amar takara juyawa waje na'eema wance take ta faman watsa mata kallon banza tace ina kwana yaya na'eema"? Mtss...Na'eema taja tsoki hade cewa da ban kwana ba kya gani munafuka kawai, ta raba gefen raheela ta wuce tana kai wa kofar da za ta shige ainihi gidan, ta labe tana leko su, raheela tasauke ajiyar zuciya cikin bacin rai wanda ita batasan lokacin da ya lullube ta ba tafara magana, kana kallo zazzafa kiyayyar da ta wanzu tsakanina da 'yar uwa ta kuma kaine sila, yaa Amar miyasa yaya na'eema takasa gano cewa duk wani furucin Ka akaina ba gaskiya bane"? Shin in har da gaske kana sona miyasa ka aure yaya na'eema"? Batare da tajira amsa da zai bata ba tacigaba da magana hawaye na zuba akan fuskar'ta, shin ita yaya na'eema wannan bai esa hujja da za tagano cewa Kayi, amfani da kalma so akaina ne domin ka tarwatsa min farin ciki ka kuma rura wutar gaba a tsakani na da ita, na roke ka yaa Amar ka sanar'da matar ka baka sona ka tsane ni ka fada mata cewa babu wata halitta da ka tsana, ka ke nunawa zalla kiyayya iri na koda hakan zai dawo da kyakyawa alaqa da ke tsakanina da yaya na'eema, takarasa zanceta tana mai rushewa da kuka mai sautin gaske yayida hawaye da majina suka chakude akan fuskar'ta. Tun lokacin da raheela tafara magana Amar yake kallon'ta zuciya'rshi, cike da takaici'n ashe duk wannan hauka da yakeyi akan raheela ita bata dauke shi, a matsayin SO ba kenan har yanzu raheela kallon makiyi take yi min, yasauke ajiyar zuciya wani iska mai zafin gaske yafito daga bakin'shi, zuciyar'shi na tafarfasa ya bude bakin'sa da kyar yanayi sa tamkar na mai ciwo hakora, yace duk abunda zan fada miki a yanzu bashida amfani raheela, iya abunda zan iya cewa da ke ni ba makiyi ki bane ni masoyi ki ne na hakika, nafara son'ki raheela tun ranar'da da ki ka fado duniya shin ta yaya za ki danganta hakan da kiyayya"? Yadago fuskar'ta da ke sunkuye tana kallon kasa ya zare lollipop din da ke ciki'n bakin'ta wasu yawu masu yauki su ka lullube lollipop din, ya kuma ciro farin "handkerchief ya goge mata hawaye masu hade da majina a zuciya shi yace raheela rigima duk, wannan kuka da akeyi lollipop na makale a baki a, baiyane kuma sai, yace banaso kukan ki raheela domin yana kona mini rai nayi miki alqawali zan dai-daita tsakani ki da na'eema kinji"? Batare da raheela ta kalle shi ba tadaga kai ta kuma juya ta nufi, gate yayida shi kuma ya bi ta da kallo, daga bisani yajuya jiki ba lakka yashiga part din iyayye shi. na'eema da ke tsaye tana kallon abinda yawakana a tsakani su ta toshe bakin'ta sakamako kuka da ya kunbuce mata, da gudu takarasa shiga gida direct falon umma hajara tafada umma hajara da ke zaune tana fama da dinbi mamaki furucin raheela, sai kawai ta ga na'eema tafado gaban'ta, tana kuka rija-rija kamar ranta zai fita. Tsoro hade da firgici suka sami mazauni akan fuskar umma, cikin sarkewa halshe tace na shiga uku ni hajara Allah yasa ba watan kunyar mu ne ya tsaya ke daina wannan kuka nake wanda bashida amfani ki warware min zare da abawa tun kafin Zuciyata, ta yi kuli-kuli kubra ta fado gabanki"? Na'eema ta tsagaita da kuka da takeyi tace yaa Amar da raheela s....da sauri umma ta zabura ta rufe mata baki tace karki ce komai tashi mu shiga daki kada ki fada yafada kunne makiyi su yi mana gori ta riko hannaye na'eema su ka shige bedroom din'ta ta zaunarda ita a gefe gado ita ma takai zaune tace inajinki na'eema, fada mun abinda Amar da annoba su kayi miki wanda ya hadasa miki wannan kukan na bala'e. Nan take na'eema ta kwashe abunda yake faruwa, tun daga ranar'da ta dire gidan Amar kalar wulakanci da yanka kauna, da yakeyi mata duk ta dalilin raheela tana dasa aya umma lailayo asshar ta durawa raheela, sai faman huci takeyi tabbas tsugunna bata kare ba, ya zame mini dole na koma waje boka duguzuu, ko ta wane hali sai naga bayan raheela, na'eema ta karbe zance ta hanyar cewa umma ahalin yanzu na fi so gani bayan raheela banaso na cigaba da gani raheela tana numfashi, kirka saka tausayi a zuciyar'ki so nakeyi raheela ta zama gawa ko kuma takarasa rayuwata a bola tana tsice-tsice, dole raheela ta mutu ko ta haukace umma domin shine hukunci da yafi dacewa da ita tashiga rayuwa ta da yawa, in bacci mijina yakeyi sunanta yake kira in kuma yana falke sam baya gajiya da anbato sunanta, inda kuma ya yi tarayya da ni da sunanta yake kira na, kodai boka nisanta zuciyar Amar daga kanta ko kuma ta mutu ko ta haukace, domin shine hanyar da farin ciki na zai wanzu nima, na dandani dadi da ma'aurata suke ji a gidanje aure su, takarasa zanceta hade da rushewa da wani irin rikitace kuka. Da kyar umma tayi nasara shawo kan'ta tadaina kuka umma tace Ki kwatarda hankalinki, ki zuba ido kisha kallo za ki ga irin mumuna hukunci da zan dauka a yanda zuciyata ta cika da tsanani kiyayyar raheela ko wane irin aiki zan iya aikatawa akanta tashi maza ki bi mijin'ki ku tafi tun da kina da ni matsalar ki ta zo karshe, na'eema ta mike, tana sharar hawaye umma ta mara mata baya suna fitowa su kaci karo da Amar da aunty amarya zaune a babban falon suna fira, Amar ya gaida umma ta amsa adakile daga bisani, Amar ya mike yace aunty za mu tafi" Aunty amarya tace to Amar Allah ya tsare ya kai ku lafiya" Amar ne kadai ya amsa da Ameen!" Da suka yi sallama Amar yadauki hanyar abuja zuciya'rshi cike da kunci musanman in ya tuna kalaman raheela da kuma wanda kaka tafada masa lokacin da yashiga bangare ta domin ya yi mata sallama, tafiya kurame su kayi Amar "driving kawai yakeyi hade da tunani raheela yayida na'eema ta kifa kanta tsakiyar cinyoyi ta tana tunani makomar rayuwar ta..... [9:11PM, 5/31/2016] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~4⃣8⃣~ Gani shiru nasu ya yi yawa yasa Amar ya kunna tape yasaka kira'a al'qur'ani mai girma ya kuma jefa lollipop" din da ya karba daga hannu raheela cikin baki'nshi yana tsotsa a hankali, abunda yakara jefa na'eema ciki gagarumi tashi hankali, saboda ta ga lokacin da Amar yaciro "lollipop din daga bakin raheela, ta ja tsoki mtwww...ta kuma galla masa harara yayida Amar "driving kawai yakeyi bai ma san tana yi ba. Raheela na fita, ta nufi gidan su zainab a bakin gate din gidan taci karo da Zainab, kallo daya Zainab ta yi mata tagano cewa ta ci kuka me ke damu ki raheela naga kamar kiyi kuka"? Raheela tasauke ajiyar tace bari kawai zainab ina gani kamar hero yana da matsala a "brain din'shi Zainab ta kyalkyale da dariya tace, laifi me ya yi miki ne ko dukanki ya yi saboda nasan duka ki ba ya yi yiwa "hero wuya"? Mtsww...raheela ta ja tsoki hade da cewa, da yake ni jaka sa ce dole yadake ni, ke matsala ki kenan ba ki iya shan labari ba, raheela takarasa zanceta tana murguda baki. Zainab takara kyalkyalewa da dariya tace fada tsakani ki da hero raheela ba ya qarewa, raheela ta tabe baki tace, umhh...nan take ta kwashe abunda yafaru tsakani ta da yaa Amar tafadawa zainab, saida suka share tsawo dakika uku zuwa biyar sannan Zainab tace, ni fa tuni nagano cewa hero yana sonki raheela, musanman wasu lukuta ina lura da irin yanayi kallo da yake miki da fitinanu idanu shi nagane kallon SO" ne. Har Zainab takarasa magana raheela take mata kallo uku saura kwabo daga bisani tace kema bakida hankali Zainab ko kin manta tun ina yarinya yaa Amar yake nuna mini zazzafa kiyayya, ke ma da ki ke qawata ya sha siya miki abu ni yahana ni ko nayi ko banyi ba yaa Amar sai yanemo laifi yadaura min don kawai yadake ni babu komai tsakanina da yaa Amar daga duka sai hantara ko yanzu ya furta yana sona ne don yarabani da farin ciki ya kuma datsi kyakyawa dangantaka da ke tsakanina da yaya na'eema kuma ya yi nasara. Zainab tace ke ce ki ke kallon hakan a matsayin kiyayya. Raheela takara harzuka cike da jin haushi furucin Zainab tace to ya eshe ki haka banaso ki Kara cewa komai, Zainab tayi murmushi tace shikenan nayi shiru da wannan zance suka karasa islamiyya. ************************ ABUJA******** Tun daga lokacin da su Amar su ka esa garin abuja, ya nunawa na'eema bedroom din'ta bata kara sanya shi a idanu'ta ba, gani yunwa za tayi mata lahani yasa ta yanke shawara shiga kitchen ta nemawa kan'ta abunda za ta ci tadafa indomie ta dan tsakura sama-sama ta kuna kayan kallo ko za su rage mata zaman kadaici da takeyi Sai misali karfe 10:08 na dare Amar yadawo yashigo falo hannu shi rike da leda mai dauke da take away" ya mikawa na'eema ya nufi upstairs inda badroom din'shi yake har yafara haura stairs na'eema tadakatarda shi ta hanyar cewa, ka tsaya mu ci abinci saboda ni yunwa nakeji, batare da yajuyo ba yace ki ci kawai naki ne ni naci nawa, yana karasa zance'sa da dan gudu sa ya hura stairs" din. na'eema tasauke ajiyar zuciya, hade da bin shi da kallo daga bisani tanufi kitchen ta dauko "plate ta juye abinci ta cika tumbi ta tana karasa cin abincin ta nufi bedroom din'ta tasakewa jikinta "shower ta shafe jikin'ta da lotion ta dan shafa powder" da lips clove" ta dauko wata fitinaniya night gown pink & white colour" ta kawata jikin'ta da ita turare kuma ita kan'ta batasan adadi da tafesa, ta dauko wani chingum" ta jefa shi ciki'n bakin'ta ta nufi bedroom din Amar ta murda handling tashiga dakin yana tsaye gaban mirror yana fesa turare tashigo kallo daya ya yi mata yadauke kai sakamako wani yanayi da yafada, tanemi gefen gado ta zauna tana tauna chingum tana lumshe idanu da yake chingum din yana kara motsa sha'awa ciki'n dakika biyar zuwa bakwai tasoma fita daga haiyyaci ta Amar karasa bisa gado ya kwanta da sauri na'eema tafada kan'shi tasaki kuka makirci me nayi maka yaa Amar, da ka ke fushi da ni tun da mu ka shigo garin abuja kafita bakadawo ba sai yanzu"? Kamshi turare ta ya hadasawa Amar jin tsanani sha'awar ta nan take ya lalube bakin'ta yasoma aika mata da sakoni masu tsanani zafi tuni na'eema takara didicewa, da kyar Amar ya iya mika hannu shi yakashe bed side lamp" ranar na'eema ta taki sa'a Amar ya rinjaye zuciya'rshi bai kirata da suna raheela ba, hakan ne yasanya na'eema farin ciki maras misaltuwa, don haka ta ji kamar ace dare shine first night" din'ta. WASHE GARI****** A garin kaduna kuwa tun da sanyi safiya umma hajara ta dauki hanyar kauye da boka duguzuu yake, umma zaune a gaban kwaya tsafi boka duguzuu, tana Kallon shi, yana ta faman tsoki burutsu, daga bisani ya kece da kazamar dariya ya zaro jajaye idanu shi masu matukar ban tsoro da firgitarwa ya kuma bude bakin'sa mai tsanani wari hade da hamami kamar moshi jaki yace........ Jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:37 am] Jeeddah Aliyu🌹: [2:12PM, 6/3/2016] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~4⃣9⃣~ Keee" wace irin sakarai ce shashasha ya za'ayi aljana inna ta wahala ta nemowa 'yarki gurbi a ciki'n zuciyar Amar amma ki ka yi sake da laya da mu ka baki har kaka raheela ta yi nasara kona ta bakisan cewa wannan laya ita ce za ta hadasa kiyayyar ta zuciyar Amar, sauki ki daya asiri da aka yiwa amar yaso na'eema bai karye ba da, sunan yar'ki wulakantata,domin wulakanci da za ta gani sai yafi wannan, karbi ya mika mata wata batta mai lullube da fatar maciji, yace wannan sunan shi, manta kowa, matsi akeyi da shi daga zarar Amar ya yi tarayya da yar ki shikenan ba zai kara tunani kowace 'ya mace sai yar'ki hatta da mahaifiyar'shi zai manta da ita{wa'iyazubillah Allah yashiga tsakani mu da bin tafarki shedan} amma ina gargadi ki da babbar murya ka da ki sake Amar da raheela su kwana daki daya matukar, hakan tafaru asiri ki zai tona. Tun lokacin da boka duguzuu yafara zuba umma ta ke masa kallon hadari kaji gani ya yi shiru ya kuma tsare ta da tula-tula idanu shi, yasa tace haba boka ko da yaushe, gargadi akan kalma daya ne kada na saki Amar da raheela su kwana daki daya me zai sa su kwana daki daya sai kace 'ya'ya hasarari"? Duk banaso raheela ban ki ace tadawo magajiya karuwai, amma bana tunani za ta iya aikata masha'a don haka kadaina wannan gargadi naka maras ma'ana balle fa'eda, umma karasa zance'ta hade da ya motsa fuska. Cikin zafin rai hade konar zuciya boka duguzuu yadaka mata tsawa, kee bakar ja'ira ni za ki yiwa bakada ko kin manta da baza ta ki ke rawa in ki ka kaini bango na juya miki baya hatta, da uwar'ki mai datti dan kwali wance ko wanke baki batayi sai bala'e da masifa ta sun shafe ta har ni za ki kalla ki ce wai su ba 'ya'ya hasarari ba ne in har su ba 'ya'ya hasarari ba ne ae ke da 'yar ki 'ya'ya harasa ne duk mutumi da shedan ya kadawa gangar sa dole don ubansa yadaka rawa a fada boka duguzuu mai aljana inna da aljana barahaza, don haka ki kiyaye ni tashi maza ki bace mini da gani,tun kafin na chanza shawara nayi miki wanka alkaba'u. Ae kuwa umma naji boka duguzuu ya abace wanka alkaba'u ta mike da sauri jikin'ta na bari ta zazzage masa Jakarta har ta juya sai kuma ta dan dakata a bakin kofar bukka tace boka ya zance haukata, raheela"?boka duguzuu ya galla mata harara ya ce babu shi domin kin riga kin bata rawarki da tsalle, sai ki je ki yi amfani da iya abunda ki ka samu daga gareni, dole ta fice domin tana tsoro fushin dan asarariya a zuciyar'ta tace shege duguzuu bakin al'muri mai siffar 'yan wuta yanzu duk wani buri da na zo da shi akan raheela yatashi a banza, amma ba komai ae sannu-sannu bata hana zuwa saidai ajima ba'a kai ba da. daga fadar boka duguzuu umma hajara ta zarce garin abuja kaitsaye gidan Suwaiba ta yada zango, bayan sun gama gaisawa da suwaiba nan umma tafara bata labari dalili zuwan ta Abuja, suwaiba ta yi ihu hade da shewa su ka tafa ita da umma daga bisani, suwaiba tace shawara da zan baki kada ki sake ki je gidan yanzu domin Amar zai iya dasa aya tambaya akanki, mafi al'khairi a tare da ke, ki bani guzuri'n ni zan karasa saura aiki, umma hajara ta yi murmushi ta zuge katuwar handbag dinta tafito da guzuri boka ta miqawa, suwaiba tace ki tabbata wannan saqo ya esa hannu na'eema yau dinan domin kinsan ba'a bori da sanyi jiki, Suwaiba ta kyabe baki, tace Ramlat na dawowa daga "school zan danka mata shi, ta kai mata da haka umma hajara tajuyo garin kaduna. Raheela da kaka na zaune a falon yayida raheela take ta faman buga "game na zuuma a wayarta, kaka tace, wai raheela ba za ki ajiye wannan 'yar banza wayar nan ki dauki littafi ki, ki yi karatu, salon kuma gobe ki eshe ni da surutu kinada jarabawa bakiyi karatu ba. Raheela ta turo baki hade da cewa ke dai kaka na fahimci kin kula kyakyawa kiyayya da wannan waya, nima ba don son da nakeyi mata ba da tuni na mayar wa yaa Amar da tsiyar'sa, kaka ta tabe baki tace anyi ba'ayi ba daukar makaho hoto, raheela ta kyalkyale da dariya daga bisani tace in banda wauta me zai kai makaho daukar photo"? Kaka tayi murmushi, batare da takara furta uffan Ba tacigaba da kallo da ta ke yi, gani haka yasa raheela tacigaba, da fadar duk lokacin da na tuna yaya na'eema na fushi da ni banaji dadi, kuma na tabbata wani abu da na'eema ta ke yi min kai gani kasan saka ta akayi saboda ba hali ta bane, shiyasa har abada ba zan daina yiwa yaa Amar tofi Allah ya esa domin shine silar kawo sabani tsakani na da ita raheela ta karasa zanceta tana mai zubarda hawaye. Kaka taja tsoki mtwww...hade da cewa kuruci dangin hauka lalle raheela kurciya na damu ki wannan shi, ake kira rashin sani yafi dare duhu, kafin ki yiwa Amar Allah esa kifara daga kan na'eema da uwar'ta hajara domin su ne bakake munufukai, marasa tsoro Allah" ae ni kallo su kawai nakeyi jira nake naga iya gudun ruwan su don haka tsakani ki da Amar ido banaso nakara ji kiyi mishi Allah ya esa. Raheela tasauke numfashi cike da rashin sani inda kaka ta dosa tace, ni fa kaka ban fahimce ki ba"? Kaka dan murmusa tace a hali'n yanzu ba za ki fahimce ni ba raheela amma lokaci na zuwa, da za ki fahimce inda na dosa don haka mu ajiye wannan zance ki tashi ki je debo abinci ki ci banaso zama da yunwa, raheela ta mike tsaye ta nufi kitchen zuciyar'ta cike da wasiwasi abunda kaka take nufi da wadanan kalamai nata masu kama da halshen damo. ABUJA************ Ramlat ta danno hanci mota ta a farfajiya gidan Dr Amar matawalle, ta nufi parking space" ta yi parking tafito daga ciki'n Mota tana sanye da wani tsadade leshi wanda akayi wulakantace dinki, ba mayafi a jikinta sai wata katuwar "handbag" rike da hannu'ta na hagu, har tajuya za ta shiga cikin gida taji anyi horn" da sauri ta mayar'da hankali ta bakin "gate" gani wanda ke Cikin motar yasa taja tayi tsaye har yakaraso sai wani murmushin yaudara ta ke yi Amar yafito daga cikin motar'sa yana rike da briefcase" kallo daya ya yi mata yadauke fuska cikin kwarewa da bariki Ramlat tace barka da zuwa Dr" Ya yatsine fuska amsa a dakile yauwa, ya yi sauri yashige cikin gida, yayida Ramlat ta bi shi da mayatace kallo daga bisani ta juya ciki'n mugun nufi tashiga gida. Kaitsaye Amar ya zarce bedroom" dinshi hakan ne ya bawa Ramlat damar zaiyanewa na'eema yanda za tayi amfani da guzuri, boka duguzuu ciki'n tsanani jin dadi na'eema tace lokaci ya yi da nima zan shana a gidan aure na tabbas raheela tashiga rayuwa ta da yawa shiyasa ni ma banida buri da wuce naga bayan'ta, Ramlat ta tabe baki tace ni dai tashi ki kawo min ruwa nasha, ciki'n zumudi na'eema ta mike ta ajiye phone" din'ta bisa kujera da tashi akai tashiga kitchen da sauri Ramlat ta mika hannu tadauki wayar, tashiga "contact" tafito da ta, ta daga handbag tadauki wata number" ta mayar'da wayar inda tadauko ta, na'eema tashigo da tray" a hannuta ta ajiye shi bisa "stool" ta tsiyaya lemo a cup" ta miqawa Ramlat, a yatsine Ramlat ta karba ta dan kurba sau biyu ta ajiye ta kuma mike tsaye, tace ni zan wuce saboda naga Dr yadawo na'eema ta yi murmushi tace na gode Ramlat ki gaida aunty, za taji Ramlat tafada kaitsaye yayida na'eema ta nufi bedroom din Amar zuciyar'ta fal farin ciki. *****BAYAN SATI BIYU***** Tsafi gaskiya mai shi domin yanzu na'eema ta mallake Amar sai abunda tafada, tuni Amar ya manta da wacece raheela ko sunanta bayaso ji, hankali na'eema ya kwanta tana cin duniyarta da tsinke, Amar yana matukar sonta kamar ya yi haukata yayida ita kuma take mishi biyayya hade kissa da kisisina saidai su ka share wata biyu sannan su ka waiwaye garin kaduna, kwana daya su kayi tak su ka juyo birnin tarayya na'eema ta yi matukar jin dadi saboda har su ka dawo Amar bai hadu da raheela ba....... [6:14PM, 6/3/2016] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~5⃣0⃣~ A kwana a tashi asara mai rai gashi har raheela ta kamalla "secondary school" a lokacin ta cika 18 yrs a duniya duk wani alama na budurci yakara baiyana a jikin'ta tsanani kyaun ta yakara fitowa, tana kwance a falon kaka tana karanta hausa novel a phone dinta, ta shagala da abunda takeyi sam bataji shigowa mutum a falon ba sai jin tayi a fisge waya daga hannu ta, a firgice ta mike zaune idanuta su ka sauka bisa fuskar nazeer ta galla masa harara tace miye haka"? Nazeer ya yi murmushi yace kina jin dadi ki tawan tun lokacin da ki ka gama secondary school" bakida aiki yi sai danna waya, raheela ta tabe baki tace to miye matsalar ka da hakan"? Nazeer yace babu, amma ina tausayawa wannan waya, raheela ta yi murmushi tace ni dai dan Allah bani phone dina, nazeer ya mika mata wayar yanemi daya daga ciki'n kujeri falon ya zauna yace ina kaka"? Raheela tace tana daki, Nazeer yace ina zance mu ya kwana"? Raheela ta murtuke fuska cikin tsiwa tace bansaniba ni fa banaso damuwa akan wane dalili za ka zabi kadinga takurawa rayuwata, da chan kasan kana sona miyasa ka aure bahijja"? Kafita daga hanya ta ko na hadaka da kaka tana karasa zanceta ta mike fuuu..tashige dakin kaka tabar nazeer zaune dafe da kai, tana shiga daki'n tafada bisa gado kaka da ke zaune bisa "pray mat" tadago ta kalle raheela tace ke kuma me da wa"? Raheela ta turo baki tace umhh..gani tayi shiru yasa kaka ta kyale ta. *****ABUJA***** Kasancewa yau juma'a Dr Amar yana saurin tashi daga "hospital" tun around 12:30pm ya nufi gida a falon yatarar'da matar gidan taci 'yar uban make up" ta yi matukar kyau tana gani shi, ta mike ciki'n shagwaba tafada bisa kirjin'shi shi kuma ya rungume ta yana shafar bayan'ta yace kinyi matukar kyau my wife" Na'eema ta kada kwayar idon'ta tace thanks hubby" yana rike da hannu'ta suka haura "stairs zuwa bedroom dinshi, yashiga wanka yayida na'eema ta bude wardrobe" tafito masa da farar shada sai daukar ido takeyi, Amar da ke bathroom yana wanka ya ji gaba daya ya yi garin kaduna, don haka a gaugauce ya cucuda jikin shi ya karewa bathroom din kallo bai sami "towel" din zai daurewa ba, yaja dan karami'n tsoki yafito daga bathroom din haka nan, na'eema da ke tsaye tana goge masa black sandal din'shi tadago idanuta gani Amar yafito ba kaya a jiki shi yasa ta kyalkyale da dariya, Amar ya galla mata harara yadauki "towel" din da yayi amfani da shi, da safe da ke ajiye a gefen gado'nsa yayida na'eema ta tsagaita da dariya da takeyi tace hubby yaushe za ka daina wannan dabi'a ta ka tafitowa "narked" daga bathroom"? Amar yaja tsoki mtwww..yace ba rana saboda Allah ya hadani da lazy wife" wance bataso aiki, na'eema tace to ae bani nake hanaka mayar'da towel" inda kadauke shi ba, Amar ya zura kayanshi yafesa turare "fragrance world" yajuya wurin na'eema yace ni zan tafi masallacin ki shirya da nadawo za mu wuce kaduna, na'eema ta zaro idanu tace lafiya me za mu je yi a kaduna"? Weekend" za mu yi Amar yabata amsa kaitsaye. Bata fuska tayi kamar za ta fashe da kuka tace haba hubby wannan wace irin bakatatan ba sanarwa gaskiya ni ban shirriyawa zuwa kaduna yanzu ba saboda gobe ne za'ayi birthday party" din Ramlat kuma kasan a gidanan za'ayi don haka za ka iya tafiya kai kadai, batare da Amar ya furta komai ba yajuya yafice daga daki'n. Misali karfe 2:03pm Amar yadawo daga masallacin yahada komaitsa shi yadauki hanyar kaduna. *****KADUNA****** Alhaji Muhammad matawalle da dan Uwanshi Alhaji Abdullah matawalle suna zaune a falon kaka suna fira raheela tafito daga bedroom ta ci kwalliya cikin shadda galila Yellow colour" dinki Riga da siket dinki yasha stones work na red colour stone's" tayi rolling" da red veil" kafarta sanye da plat Shoes suma red colour" jikin'ta na fitarda Qamshi hadafiyar humra hadin 'yan maiduguri takaraso falon ta durkusa ta gaida Abba da daddy. Daddy yace mama naa na nemo miki admission" a "American beze university abuja" Monday insha Allah zan tafi da ke nayi miki registration" za ki karanci medicine" raheela ta zaro idanu tace umhh..daddy ni fa banaso "course" mai wahala daddy ya yi murmushi hade da cewa ba wani wahala nasan za ki iya mama naa, ina buri bude hospital domin taimakawa al'umma musulmin da kuma wanda basuda karfi zan mika al'haki kula da hospital din a hannu yaya'nki Amar kinga dole Muna da bukatar kwararo likitoci shiyasa na zaba miki wannan "course gaban raheela yafara dukan uku-uku sakamako sunan Amar da taji daddy ya kira jin ta tayi shiru yasa daddy yace kinyi shiru bakice komai ba mama naa"? raheela tayi dariya yake tace shikenan daddy na gode Allah yakara budi, cikin tsananin jin dadi daddy amsa da Ameen"! Raheela ta juya wurin Abba taa tace Abba kai kuma dalleliya mota za ka siya min, Abba ya dan murmusa yace maama rigima me za ki yi da mota ke da ko "driving ba ki iya ba. Abba bala driver yace zai koya min, Abba yace shikenan Allah yabani ikon siya" Tace "ameen Abba naa ta mike tsaye hade da fadar kaka na tafi gidan su zainab batajin dadi na duba ta kaka tace adawo lafiya amma karki anjima toh..kaka raheela tafada hade da ficewa daga falon. Raheela tashiga gidan su zainab da 'yar gajeriya sallama, zainab tafito daga daki'nta fuskar'ta a sake tace bakida kirki raheela sai yau ki ka ga dama zuwa duba ni raheela tayi dariya tace kai na bisa wuya qawata ayi min afuwa, Zainab ta tabe baki tace nayi ba don halin'ki ba, su ka karasa daki'n maman Zainab, raheela ta gaida ta daga bisani su ka zarce daki'n Zainab suka bude "chapter" fira anan raheela ta sanar'da Zainab daddy yasamo mata admission" Zainab ta tayata murna da sauri raheela ta mike tsaye tace na shiga uku 5:30pm tayi nasan halin kaka sai tayi min fada, Zainab ta tabe baki tace sai kace da gaske din kina tsoro kaka, raheela tayi dariya hade da daukar mayafi'nta tace ko bana tsorota ina tsoron masifar'ta, Zainab tace mu je na rakaki, suna zuwa gate raheela tacewa zainab tsaya daga nan tun da bakida lafiya da haka su kayi sallama, raheela tanufi gida. Tana shiga falon kaka su kayi 4 eye's ras-ras sautin da ke fita daga kirjin raheela kenan, ciki'n sanyi jiki takarasa shiga cikin falo da kyar ta iya bude bakin'ta tace ina wuni yaa Amar"? A dakile ya amsa mata, batare da ta zauna a falon ba tanufi bedroom" yayida Amar yabita da kallo..... Jeeddah Aliyu🌹🌹 [18/06 8:37 am] Jeeddah Aliyu🌹: [10:28AM, 6/4/2016] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~5⃣1⃣~ Yasauke gwaron numfashi yajuya karaf suka hada ido da kaka da sauri ya sunkuyarda kan'shi kasa, kaka ta tabe, baki tacigaba da fadan da takeyi masa, baka dauko gaskiya ba Amar ace sai ka share tsawon watani daya-daya har wata bakwai ba tare da ka zo ka gaida iyayye ka ba duk 'da nagari yana neman albarka iyayye sa, magana ta karshe da zan fada maka, ka dage da addu'a Amar domin bakasan adadi mutane da suke binka da mugun nufi Allah ya tsare ka ya yi mana jagora. Ameen" na gode kaka insha Allah zan kiyaye abunda ki kafada min. Shikenan tashi kashiga sashe {part} iyayye naka ka ba mahaifiya'rka hankuri domin tafi kowa shiga yanayi na damuwa, akan rashin ka, na tabbata ko wannan zuwa da kayi addu'a da mu ke yi akanka ne Allah ya amsa ya karkato mana da hankali ka. Cikin yanayi na mutuwar jiki Amar ya mike tsaye, ya yi kasa da murya yace kaka, wannan yarinya da tashiga bedroom dinki kamar raheela, Ciki'n tsanani mamaki kaka take kallon shi daga bisani tace ba kama bace Amar raheela ce, kenan ita ma anyi nasara juya maka kwakwalwa ka manta da ita ke duniya ina za ki da mu miyasa wasu mutane suke da dan banza son zuciya"? Amar ya yi tsaye yana mamaki wannan furucin na kaka, yace kaka me ke faruwa ne"? Girgiza kai tayi tace ba komai Amar je ka kasami albarka iyayye ka, in lokacin yayi kai da kan'ka da kuma ahalin gidanan za ku fahimci abunda yake faruwa, batare da yakara furta ko kalma daya ba yafice daga falon kaitsaye yanufi part din iyayye nashi, yana shiga falon yaci karo da mamee za ta shiga kitchen" gani shi yasa mamee tayi tsaye sororo tana kallon shi, da sauri yacire takalmin kafar'shi ya esa wurin ta ya qanqame ta yafeshe da kuka kamar karami'n yaro yace, am sorry mamee please forgive me, I will never repeat it's again" Mamee da idanuta suka ciko da kwalla tsanani tausayi Amar yakamata, ta bubuga bayan shi tace is okey Amar ya wuce sai ka kiyaye gaba, Amar yakara qanqame ta yace thanks" my special mom" cikin dariya mamee ta kai masa duka tace to ae sai kasake ni koh, Amar yana dariya yasaki mamee, yanemi kujera ya zauna, mamee kuma tashige "kitchen fuskar'ta dauke da tsantsan farin ciki, lantana ce tashigo falon da sallama tana arba da Amar tadaka tsalle hade da ihu kiran sunan shi, lah ga likita, mamee fito ki gani ga likita nan ya zo, Amar ya yi dariya ya girgiza kai yace lantana kenan to karaso mu gaisa yafi wannan zarar ido da ki keyi kamar mayya lantana takaraso sannan, ta gaida shi ya amsa mata ciki'n sakin fuska, mamee tafito daga kitchen hannu ta dauke da katon "tray da sauri lantana ta karbi tray daga hannu'ta ta dire shi bisa "stool" din da ke gaban Amar ta juya tanufi daki'n da aka ware mata. mamee tayi "serving" din'shi yana cin abinci suna fira. Ta bangare raheela kuma tana shiga daki'n ta zube bisa gado, tana sauke numfashi kamar wance ta yi tsera gudu, a zuciyar'ta me wannan fitinane yazo yi"? Gaskiya ni kan banyi farin ciki da zuwan shi, ba mtwww..taja tsoki ta diro daga bisa gado tanufi kofar falo sakamako ta ji yafita, ko zama batayi ba tafara aikawa kaka da tambaya kaka me wannan dan duniya ya zo yi ne"? takarasa magana tana yatsine fuska. Batare da kaka ta kalle ta ba tace ina ruwan'ki da shi ko kina bin shi bashi ne"? umhh...kaka kenan in dai yaa Amar ne ba ki kama kowa ba, raheela tafada tana mai tabe baki, ta mike tsaye ta fice daga falon tanufi, bangare su a falon tarar'da aunty amarya tana kallo wani shiri mai take girki adon uwargida wanda salma suleiman take gabatarwa, raheela na zama idanuta suka sauka bisa akwatin talabijin tace "wow! Aunty na Salma suleiman kinyi matukar kyau tamkar sarauniya, aunty amarya ta tabe baki tace kinsan ta ne"? Raheela ta kada kai, aunty amarya tace a ina ki kasanta"? A talabijin mana, raheela tafada kaitsaye, aunty amarya tayi murmushi saboda ta fahimci shirme ta ne ya motsa don haka tacigaba da kallonta. Yanda raheela ta kurawa tv idanu dole taba mai karatu dariya tasaki baki da hanci, tana kallon salma Suleiman har salma ta kamalla shiri ta raheela ko kwakwara motsi batayi, raheela tasauke ajiyar zuciya, ta juya wurin aunty amarya tace aunty yaushe za ki yi mana wannan girki"? Ke ba ki iya shiga kitchen bane da ba za ki girki da kan'ki ba"? Sallama da akayi ce ta katsiwa raheela magana da ta je fada, cikin fara'a da walwala aunty ta amsa sallama hade da cewa wa nake gani kamar Amar"? Amar yakarasa ya zauna ya sunkuyarda kai alamar jin kunya yace mu same ku lafiya aunty"? Lafiya qalau Amar ina su na'eema"? Lafiya qalau na baro ta" Allah sarki ashe ba tare ku ka zo ba"? "eh tana da dan uzziri shiyasa na zo ni kadai tace a gaida ku, mu na amsawa maama tashi ki kawowa yaya'ki ruwa" da sauri Amar yace na koshi aunty daga part din mamee nake ta cika min ciki, da girki mai dadi, yakarasa zance'sa yana dariya aunty ma ta dan dara, raheela kuma ta mike da nufi tafita daga falon aunty ta katsi mata hanzari ta hanyar cewa baki ga yaya ki bane da ba za ki gaida shi"? Raheela ta langwabe kai ta marairaice murya kamar za tayi kuka tace..... [10:01PM, 6/4/2016] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 ~5⃣2⃣~ Aunty na gaida shi a part din kaka, ta juya waje shi, tace "koh Yaa Amarrr"? Yanda taja sunan nashi ya hadasawa tsiga jikin'shi tashi yarrr....ya yi namijin kokari ta hanyar tattaro natsuwa shi ta wance gadin yace, uhmm...aunty ta gaida ni, aunty tace oya shiga "kitchen" ki kwashe min tuwo, raheela ta turo baki ta juya tashiga, "kitchen" Amar sai bin ta da kallo yakeyi, tana shiga kitchen batafi 5 minutes ba ta kurma ihu tana kira wayyo aunty hannu na, kafin aunty ta mike tuni Amar yariga ta kai wa "kitchen tana durkushe rike da hannu hawaye na zuba, da sauri Amar ya durkusa gaban ta yariko hannu nata, ciki'n sarkewa halshe yace sannu raheela" Ta balla masa harara ta kuma murguda baki, a zuciyar'shi yace lalle zafin tuwo bai ratsa ki ba tun da har kina iya murguda baki, baiyane sai yace da zafi koh"? Kafin ta bashi amsa su ka ji sautin murya aunty amarya tana fadar, ke dai maama yaushe za ki yi hankali, garin ya ya ki ka kone hannu ki"? Amar ne yakarbe zance ta hanyar cewa ae ba sosai ta kone ba, aunty tace shine don tsabar iskanci ki ke yi mana wannan uban ihu"? Raheela ta fisge hannuta daga riko da ya yi mata, ta mike tsaye tace don ba yana jikin sa bane shiyasa yafadi haka. Ke dai tsabar raki ne kawai irin naki, Amar yafada yana dariya, raheela ta tabe baki tafice daga "kitchen din aunty amarya tace ae maama abun kuka baya mata wuya kaka tariga ta sagarta ta. Amar yayi murmushi'n yafito daga kitchen din yace aunty, umma na ciki kuwa"? A'a batanan ta, tafi katsina wurin bikin aure, Amar yace Allah yadawo da ita lafiya" Ameen aunty tafada hade shiga kitchen" din Amar yakara cewa aunty sai anjima zan dan shiga gari' Toh Amar adawo lfy" Allah yasa Amar yafada hade da ficewa daga falon zuciya'rshi cike da muradi kara gani kyakyawar fuska raheela saidai kash koda yafito tashige "part" din kaka dole ya ja motar'shi yakara gaba. Raheela na shiga falon kaka tafara yi mata kukan shagwaba, saida kaka tayi mata tofi sannan ta yi shiru. *****DARE******* Da misali karfe 9:15 na dare Amar da daddy na zaune a hadade falon daddy mai kama da falon sarakuna, daddy na kishigide yayida Amar yake zaune kusa da shi, sai faman zuba fira su keyi har daddy ya gangaro kan zance karatu raheela yace, Amar tun da gobe za koma abuja sai katafi da raheela kayi mata registration" da duk wani abu da take da bukata kuma banaso ta zauna "hostel" nafiso ta zauna gidan'ka domin za ka fi bata kulawa da kuma karatu ta, duk abunda yashige mata duhu za ka taimaka mata. Tun lokacin da daddy yafara magana Amar yatsinci'n kan'shi da mashahuri faduwa gaba, gaba daya yarasa natsu jikin'shi ya jike da gumi kamar ba Ac a falon, ya naji kayi shiru Amar ko har yanzu kana 'yar tsama da Mama naa ne"? Da sauri Amar ya girgiza kai hade da fadar Noo" kawai ina tunani irin farin ciki da na'eema za ta nuna in taji raheela za ta zauna abuja, daddy ya yi murmushi'n su na manya yace na'eema da raheela su ne suka gado mu, domin ni da Abdullah haka mu taso, kuma har yanzu da girma yakama, mu muna da kaunar junan mu ko kaka bata gane kan mu shiyasa nake, gargadi ka Amar da rike zumuncin domin kaine babba da kai 'yan uwa ka su ke koyi don haka ina rokon ka da ka rike raheela amana kabata kulawa irin wanda mu iyayye ta za mu bata, ka kuma yi hankuri da halinta saboda kasan reno kaka ce tasaba da shagwaba daddy yakarasa zance'sa yana dariya. Amar ya sauke gwaron numfashi kamar zai shede ya hadiye wasu yawu masu masifar daci saboda yafara hango bala'e da zai tun karo shi, da kyar iya fadar "insha Allah daddy zan rike raheela amana, zan kuma bata kulawa ta musanman har izuwa lokacin da Allah zai nuna mana ta kamalla karatun ta, ae raheela Qanwa tace ta jini ko ada chan da nake tsangwama ta, ina yi ne domin ko za ta rage rashin ji da takeyi amma a yanzu "no thing's between us" Daddy ya daga kai alamar ya gansu da karya da Amar ya shararo masa, daga bisani yace shikenan zan tura maka kudi ta "account" dinka sai ka yi mata amfani da su, da sauri Amar yace haba daddy wane irin kudi kuma ko manta da matsayi na big brother" Daddy ya yi dariya yace da kyau big brother" Amar shima ya yi dariya rashin mafita a haka su ka cigaba da fira. ******WASHE GARI****** Sai a washe gari daddy yashiga "part" din kaka ya sanar'da ita tafiyar raheela, da kuma hukunci da ya yanke akan raheela za ta zauna gidan Amar, kaka tayi shiru tana juya wannan sabo al'amari a zuciyar'ta, saidai batada zabi illah ta nuna amincewar ta domin bataso ta kawo shakku a zuciyar 'ya'yata, don haka kaitsaye ta amince yayida raheela na jin zance tafara kuka, da kyar daddy ya rarrashe ta yace tashi maza ki hada kayanki yana, jira'nki kuma inda ya yi miki abunda bai gamsar da ke ba ki kirani a waya zan har gidan'shi na wanke masa allo shi, ba yanda raheela ta iya dole ta hada kayanta ciki'n katuwar trolley" daddy yakira bala driver ya kai mata trolley din ciki'n motar Amar kaka ta kira Amar su ka kebe ta ja masa kunne hade da gargadi akan raheela, daga nan raheela tayi sallama da mamee da kuma aunty amarya saboda uwar gaiyya wato umma hajara bata ga gari ballatana taga kalubali da yake tunkaro su ita da 'yarta. Raheela kuka takeyi kamar ranta zai fita saboda kwata-kwata wannan tafiyar bata kwanta mata a rai ba tana tausayawa kan'ta irin rayuwa da zatayi a gidan Amar da na'eema ta rungume kaka ciki'n shashekar kuka tace kaka banaso tafiyar nan bazan iya jure wulakanci ba, da sauri kaka ta rufe mata baki tace kiyi biyayya ga iyayye ki raheela Ki tafi kawai Allah yana tare da ke zan kuma cigaba da yi miki addu'a neman kariya daga rabbil-izzati, raheela ta juya wurin abba taa tace abba zan tafi abba yace toh mama naa kidage kiyi karatu da kyau nima zan cika alqawali zan siya miki tsadadiyar mota, raheela tadaga kai takara juyawa wurin da aunty amarya da mamee suke tsaye tace aunty da mamee za ku yi kewata koh"? ae kuwa mamee da aunty suka fashe da kuka domin raheela, tayi masifar basu tausayi saboda wannan ce tafiya ta farko da raheela ta tabayi a rayuwata, gani yanda suke kuka yasa daddy yariko hannu raheela yasakata cikin mota sai kace amarya, duk wannan shagali da akeyi Amar yana zaune cikin mota yana danna waya hankali'nshi kwance, daddy yana juyawa raheela ta balle kofa tafito ta balla da gudu ta qanqame kaka tana kuka ita ma kaka tafashe da kuka sai ga kaka da raheela na kuka rija-rija, ba mai rarrashi wani, ciki'n zafi rai Amar yafito daga cikin mota ya banbare raheela daga jikin kaka yace wai miye haka ne"? da za ku cikawa mutane kunne da ihun kuka, karatun nan ba dole bane za ta iya zamanta, kaka ta galla masa harara da Jajaye idanuta tace kai ka kiyaye ni, Amar ya janyo hannu raheela da karfi yajefa ta mota yazagaya yashiga a driver seat ya kuma yi lock'' din kofa yayida, daddy yace kai ka bita a hankali ka ji koh"? Amar ko saurare shi banyi ba yafisgi mota maigadi ya bude masa gate yafice daga gidan raheela nagani an fito, daga unguwar su takara fashewa da wani sabon kuka..... ALHAMDULLAHI"! Anan na kawo karshen littafin MIJIN 'YAR UWA TAA kashi na daya sai ku kasance tare da ni 'yar gidan shehu Aliyu bayan sallah inda Allah yanufe ni da kaiwa za kujini dauke da MIJIN 'YAR UWA TAA kashi na biyu tare da sabon littafi na mai suna NI DA YAYA HABEEB. Nice taku mai muku fatan alkhairi Allah yabamu ikon gudanarda ibadamu a cikin watan Ramadan mai albarka Ameen. I LOVE YOU OLL MY FANS😍 Jeeddah Aliyu🌹🌹 [06/07 11:01 am] Jeeddah Aliyu🌹: [02/07 8:52 am] Jeeddah aliyu🌹: [28/06 3:28 pm] Jeeddah aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 {Part 2} Goron sallah 💕love story 2016💕 Na Hauwa shehu Aliyu🌹 ~5⃣3⃣~ Raheela tacigaba da rusa kuka kamar ranta zai fita ko kallon ta Amar baiyi ba yacigaba da driving" sai faman sharara gudu yakeyi kamar Wanda zai tashi sama, har suka fita garin Kaduna raheela tana kuka gani kukan nata yaki karewa yasa Amar yataka birki da karfi cikin tsanani bacin rai ya balle kofar mota yafito ya zagaya ya bude kofar da raheela take zaune yafisgo ta da karfi ya cilla ta waje yakara bude sit din baya yafito da trolley dinta ya ajiye mata a kasa a harzuke yace ni ba dan iska bane da zan dauke ki a Mota kina mini kuka sai ki zauna anan tare da kuraye jeji kicigaba da kuka, ki dama chan kinfi dacewa da abinci kuraye yana karasa zance sa yajuya cikin zafin nama yashiga mota yafisgeta raheela nagani haka ta kurma ihu tabi bayan motarsa da gudu kafarta ko takalmi babu tadinga kwalla masa kira wayyo yaa Amar karka tafi ka barni wallahi tsoro nakeji dan Allah kadawo nadaina kuka wayyo kaka nashiga uku kuraye za su cinye ni tuni motar Amar ta bacewa ganinta dole tajuyo tanufi wurin trolley dinta wani wawa ihu tasaki hade da zubewa kasa sakamako qaya aduwa da ta, taka da Sauri ta rike kafar ta tana gunji kuka, gani jini na zubawa daga kafarta ga kuma qaya ta lutsi cikin naman kafarta yasa raheela takara shiga cikin tashin hankali da kyar ta iya mikewa tsaye tasoma dingishi ta nufi trolley dinta ta zauna akanta tasoma kallon titi tsawon lokacin ta dauko a zaune ko tsuntsu bataga wulgawa sa ba sakamako yau weekend ne mutane basu cika fitowa ba raheela tacigaba da shashekar kukanta kamar daga sama taji muryarsa yana fadar kee in kin gama kukan naki ki taso mu tafi, ni karki bata min lokacin, da sauri raheela tadago ta kalle shi, yana tsaye jikin mota babu alamar damuwa akan fuskarsa tasaki katuwa ajiyar zuciya ta Mike tsaye Sam ta manta da qaya da ke kafarta ae kuwa ta kurma razanane ihu hade da fadar wayyo yaa Amar kafata, da gudu yakaraso waje ta ya zaunarda ita a kasa ya kuma yariko kafarta yaciro qaya da karfi raheela ta dagargaje iya karfinta ta kurma ihu hade da chakumo rigar Amar rungumo ta yayi akan kirjinsa yasoma bubuga bayanta ita kuma ta lafe tana kuka kasa- kasa tsawon dakika bakwai suka dauka a haka daga bisani yadago ta yafito da handkerchief" yadaure mata kafar chan kasan makoshi yayi magana tashi mu tafi, raheela ta make kafada ya zaro idanu hade da fadar uban me zaki cigaba da yi anan"? Tayi rau-rau da idanu alamar za tayi kuka cikin murya shagwaba tace wallahi ba zan iya tafiya ba kafa na zogi takeyi kamar za ta cire Amar ya kyakyale da dariya daga bisani ya tsagaita da dariyar da yakeyi ya dungure mata kai hade da cewa raheela kin Shiga uku da raki, 'yar wannan qaya ce zata hanaki tafiya"? Raheela ta galla masa harara tace don ba yana kafar ka bane shiyasa ka ke ganinta 'ya da kaine ka takata da ihu da za kayi sai yafi nawa. Amar yayi murmushi har kumatu sa suka lotsa raheela batasan lokacin da tasaka dan yatsa ta cikin dimple" din nashi tace yeee" yaa Amar "dimple" Amar yakara kyakyalewa da dariya yace ke fa shashasha ce raheela sai yau ki ka fara gani "dimple" akan fuska ta"? Raheela ta turo baki tace kullum fuskar ka a murtuke take ta yaya zan gano kanada "dimple" Amar ya girgirza kai yace to sarkin 'yan sharri, sharri zakiyi min"? Raheela ta tabe baki hade da cewa ba sharri bane gaskiya ce na fada, yace to naji ki tashi mu tafi ko nakara tafiya na barki wannan in natafi bazan dawo ba. Raheela ta yatsine fuska tace ko yanzu da kadawo waya baka hankuri"? Da sauri ya mike tsaye yace "okey ki zauna karki tashi, ya juya yanufi mota raheela nagani haka ta Mike tabi bayan shi, tana fadar yaa Amar wannan abar waya zai dauke ta"? Mtsss.... Amar yaja tsoki yakoma yadauko mata trolley" dinta, tunda suka dauki hanya raheela keta faman korafi ni dai yaa Amar kadauki alhaki na haka kawai kasa nadinga ihu cikin jeji"? Amar ya tabe baki yayi banza da ita kamar baiji abunda tafada ba [02/07 8:42 am] Jeeddah aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 5⃣4⃣ Gani yayi banza da ita yasa ta shafawa kanta lafiya, ta lafe jikin kujera ta lumshe idanu ta tasoma tunani irin kala rayuwa da za tayi a gidan yaa Amar, da haka baccin yayi awon gaba da ita. Amar ya ji shiru nata yayi yawa ya juya Inda take zaune ya tayi bacci ya tsura mata idanu tsanani sonta yafara yawagi akan zuciyarsa, ya mika hannu shi yariko hannuta a haka yadinga driving daya hannu shi yana sarke da na raheela har suka Shiga garin abuja raheela tana sharar bacci, kaitsaye Amar yadoshe gidansa da ke maitama, yadanna horn maigadi ya wangame masa gate yanufi "parking space" yayi parking, ya kashe wutar mota yakara samu wadatace lokacin karewa raheela kallo hannu ta da ke cikin hannu shi yafara murzawa a hankali, saida yashare tsawon dakika uku zuwa hudu a haka daga bisani yafara tashe ta cikin husky voice" dinshi raheela"raheela ki tashi mu eso gida, a hankali tafara bude idanu ta tayi doguwar hamma hade da miqa ta balle kofar mota tafito tasoma karewa "compound" din gidan kallo Amar dai yana tsaye yana kallonta tace "wow! What's beautiful house I like it's" Amar ya girgiza kai ya kwadawa maigadi kira yanuna masa trolley dinta yadauka yashiga mata da ita ciki, gida yakara juyawa wurin ta yace kee in kingama shirme ki, ki zo mu Shiga cikin gida rass rass sauti da yake fita daga kirjin raheela kenan da ta tuna gidan yaya na'eema ne ta zo ta bata fuska kamar za tayi kuka, yakara cewa mu tafi mana dole raheela ta bi bayan Amar suna kaiwa bakin kofar da ke sadaka da babban falon gidan suka ci karo da na'eema da sauri raheela ta juya ta boye a bayan fila yayida hankali na'eema gaba daya yana wurin mijin ta Sam bata Lura da raheela da ke boye ba ta rungume shi hade da fadar I miss you hubby" shima Amar yakara manne ta a kirjin shi har wani shinshina ta yakeyi yace I miss you too baby" raheela da ke labe tana kallo su taja tsoki tace 'yan iska kawai kalli wani rukurkushe juna da sukayi, ko kunya basaji, ta na kallon su suna manne da juna suka shige falon aka bar ta tsaye ga gajiya ga yunwa Sam Amar ya bata da wata aba raheela saida na'eema tace hubby wannan katuwar trolley da Joseph yashigo da ita menene a ciki"? Dai lokacin Amar yatuna tare yake da raheela da sauri ya ture na'eema daga jikinsa hade da cewa "oh shirt" ya Mike tsaye yanufi kofar fita da sauri kamar zai tashi sama na'eema da ke tsaye fuskarta dauke da mamaki me Amar ya tuna da shi da yahadasa masa wannan saurin haka yana fita ya hango ta jikin fila yaja yayi tsaye yasauke ajiyar zuciya ya qura mata ido ita kuma ta murguda masa baki yayi murmushi yakarasa kusa da ita cikin sanyaya murya yace baby me yahana ki shiga ciki"? Raheela tayi rau- rau da idanu ta langwabe kai tace yaa Amar ina tsoro haduwa da yaya na'eema bansan wane irin kala maraba za tayi min ba, tsanani tausayi ta Yakama Amar yariko hannu ta yace karki damu raheela tunda nayiwa daddy alqawali zan kula da ke bana tunani akwai wani mahaluki da zai takura ki "fill free baby remember it's your hero house okey" Raheela ta daga kai alamar ta gansu da kalaman sa with full confidence" tashiga cikin gidan na'eema fito daga kitchen hannu ta dauke da hadade tray da lemon kwali akai da kuma glass cup's" idanu ta suka hasko mata fuskar raheela da Amar sun jero hannu Amar na danke da na raheela batasan lokacin da tasaki tray hannuta cup's suka sauka bisa tiles suka tararatsi ita kuma tadafe kai hade da fadar innalillahi wa'inna illahi raji'um nashiga uku ni na'eema, wace irin masifa ce yau tasauka a gida na? Babu shiri Amar yasaki hannu raheela yakarasa wajen na'eema yariko ta yace calm down sweetheart" da sauri ta ture shi idanu ta sun kada sunyi jajir tsanani tashin hankali ya baiyana akan fuskarta cikin sarkewa halshe tace you ask me to calm down yaa Amar as how just tell me as how"? Ta karasa zance ta cikin daga murya da kururuwa, Amar yadafe kanshi yasoma tunani mafita cikin zafin nama na'eema ta esa wajen raheela tafisgo ta wanke ta da mari ta kuma rufe ta da duka, tana cewa wallahi raheela ko kece 'yar sarkin matsafa na duk duniya baki esa ki rabani da yaa Amar ba don haka yau sai na kashe ki in yaso nima a kashe ni, me na tare miki da za ki zabi hanyar musgunawa rayuwata ki barni na rayu da yaa Amar domin ni nafi chanchanta na kasance tare da shi ba ke ba raheela yayida raheela sai kakari mutuwa takeyi domin ba karamar shaqa na'eema tayi mata ba da gudu Amar yakaraso wajen su yadauke na'eema da wawan mari Wanda yahadasa mata sakin raheela bata shirya ba raheela ta zube kasa numfashi ta na fita guda-guda jijiyoyi kanta sun fito radau-radau kwayar idon ta sunyi jajir, Amar yadurkusa gabanta yadago kanta yadaura bisa cinyoyi shi yace........ 💃Happy sallah💃 Jeeddah Aliyu🌹🌹 [06/07 10:58 am] Jeeddah aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 {Part 2} Goron sallah 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 5⃣5⃣ Yace am so sorry" raheela zan dauki mumuna mataki akan, wannan cin kashi da na'eema tayi miki domin ke amana ce a wurina, kiyi hankuri kitashi kinji, raheela takara fashewa da matsananci kuka tace dan Allah yaa Amar ka mayarda ni Kaduna wallahi banaso zaman gidanka domin nasan ba karamin, qalubi zan fuskanta, kafin Amar ya bata amsa na'eema ta karaf tace zai fi miki sauki ki koma Inda ki ka fito don nasha alwashi sai na kassara rayuwarki munafuka alguguma baqar makira mai buri rusa farin ciki 'yar uwa taa kaicho ki raheela da kwakwalwa ki tasa gano miki yaa Amar Mijin 'yar uwa ki ne, kuma na ran........kee na'eema ki rufe mini bakin ki tun kafin ni na qassara taki rayuwa yaa Amar ne yadaka mata tsawa dole, na'eema ta kama baki ta sai faman haki takeyi ta juya fuuu ta haura upstairs" ta nufi bedroom dinta, yayida Amar yacigaba da rarrashi raheela da kyar ya ciyo kanta tadaina kuka yacigaba da fadar tashi mu je na nuna miki room dinki, raheela ta mike tsaye Amar ya shige gaba ta Mara masa baya, saida yakaita har cikin daki sannan yajuya yafice daga dakin. Raheela ta fada bisa gado tasaki ajiyar zuciya mai karfi, tasoma tausayi kanta saboda tasan duk lokacin da na'eema tayi nassara Kara danqa ta ba, karamin cin ubanta za tayi ba gaskiya ba zan iya cigaba da juri irin wannan wulakanci ae bani nakawo kaina gidanta ba kawo ni akayi mtsss taja dan karamin tsoki, hade da mikewa zauna ta buga dan uban tagumi ta cigaba da zance zuci ni narasa me ke damu yaya na'eema ita har yanzu nata hauka yana nuna mata yaa Amar yana sona, lalle yaya na'eema karamar kwakwalwa ce da ita ko ta manta ne ni da ita uban mu daya har take tunani akwai wata alaqa da ta danganci soyayya tsakani na da yaa Amar"? Mtsss...takara Jan tsoki kalle yanda ta shake ni kamar za ta rabani da rai na tasaka hannuta na dama tana shafar wuyan nata, sai faman zogi da radadi yakeyi mata musanmman makogwaro ta da takeji sa yana fitarda wani zafi tamkar ta sha tafasashe ruwan zafi, kai ina raheela tafada a baiyane tsanani bacin rai ya baiyana akan fuskarta duk lokacin da yaya na'eema takara kuskure taba ni sai na shuka mata rashin mutunci don ni ba baiwa bace da za ta dinga jingata, duk ranarda nayi mata illah mijinta da kanshi zai mayarda ni inda yadauko ni tasaki murmushi jin dadi domin har ta hango kanta bisa ciyoyi kaka ta Mike da sauri tashiga "bathroom" Na'eema na shiga dakinta ta fisgo wayarta da ke chaji ta dannawa umma hajara kira saida tayi ringing kusan sau uku tana tsinkewa sai a na hudu umma tadauko, tana karawa bisa kunne ta sautin kuka da kururuwa na'eema yadaki dodo kunne ta a firgice tafara magana ke na'eema waye ya mutu ne"? Cikin shashekar kuka na'eema tace ba mutuwa akayi ba umma amma na rantsi da Allah gara mutuwa da wannan masifa da tasauka a gida na, wayyo umma nashiga uku na lalace watan kunyar mu da tonuwar asiri mu ya tsaya na tabbata kwano tuwo na yaqare a gidan yaa Amar cikin tsanani tashin hankali mai dauke da rudani umma hajara ta aikawa na'eema tambaya wai meke faruwa ne na'eema kiyi gagawa ki warware mini zare da abawa domin zuciyata cike take da tsantsan fargaba"? Cikin yanayi na Wanda yarasa mafita da tudun dafawa na'eema ta kwashe abunda ya wakana ta sanarda umma, tsawon dakika uku zuwa hudu umma hajara tadauko tana nazari daga bisani ta nemo abun fada saida tasaki katuwar ajiyar zuciya mai cike da konar zuciya tace amma Allah yatsinewa hajja rahee albarka domin nasan wannan quli aikinta ne, lallai a wannan karo dole na nunawa hajja kaka kuskure ta sai na hadasa mata nadama tura raheela gidanki da tayi zan shiga na fita domin na kawo karshen numfashi raheela a doron duniya sai na zamo sila goge babi ta a duniya koda hakan zai kasance nima na rasa rayuwa ta {kaicho umma hajara jahilci yariga yayi miki kanta kin kasa gano cewa babu yi sai Allah wannan shine furucin da ni yar gidan Shehu aliyu nayi yiwa umma hajara amma kuma mu je zuwa karshen alawa kasa} Saida umma hajara ta dasa aya a zance ta sannan na'eema tasamu damar kara tofa albarkacin bakinta umma ki taimake ni ki je wajen boka duguzuu yayi aikin da raheela zata mutu saboda ina ji a jikina wannan zuwan da raheela tayi kamar za kawo karshen zama na da yaa Amar, da sauri umma hajara ta katsi ta, ta hanyar fadar kul karna sake jin kinfadi wannan mumuna furuci, yanda raheela ta shiga rayuwa ki ta zamo sila hanaki rawar gaban hantsi nima na rusa rayuwa ta don haka ki kwatarda hankali ki kamar kinyi bako ya mutu a wannan karo raheela bazata kai labari gobe zan dira garin Kaduna kudi ne kawai suka zame mini dole na dauka daga nan sai fada boka duguzuu cikin tsanani jin dadi na'eema tace na gode umma naa shiyasa nake matukar sonki domin duk lokacin da nashiga damuwa kina nemo min mafita, umma hajara tayi dariya tace to wa nake da shi in bayan ke ae dole nayi fito na fito da makiyanki haka umma hajara da na'eema suka cigaba da kule-kule su nagani bayan raheela. Amar yana fitowa daga dakin raheela "direct bedroom dinshi yashiga kaitsaye bathroom yadosa yasakewa jikinsa "shower" bai dauki dogon lokacin a bathroom ba yafito yashirya jikinsa da white jeans trouser" da t-shirt blue colour" sai faman zanga qamshi turare pure blue" yakeyi masallaci ya wuce yayi sallah azhar yana dawowa daga masallaci yanufi dining table yayi saving din abinci ya dauki lemo kwali na fruitta da glass cup" nufi dakin raheela. Tabagare raheela kuma tana fitowa daga wanka ta janyo trolley dinta tafito da slick material" riga da siket tasaka sannan tayi sallah tana kamalla sallah taji hanji ta yafara kugi yunwa ga raheela batada hankuri akan yunwa dole na nemowa kaina abinda zan ci in kuma yaya na'eema tayi yunkuri tabani ni ma zan nuna mata nawa kala hauka da wannan zance zuci raheela ta mike ta nufi kofar fita karaf taci Karo da shi, da sauri ta juya ciki daki ta nemi gefen gado ta zauna yakarasa shigowa ya dire plate din hannu shi a kasa ya kura mata idanu kamar yau yafara ganinta saida ya share tsawon dakika biyar yana kallonta yayida ita kuma kanta yana sunkuye yayi gyara murya tamkar mai shirin yi kiran sallah daga bisani ya kiranta sunanta cikin sanyaya muryar mai tsanani sanyi da gardi domin raheela saida ta lumshe idanu ta raheela yakara kiran sunan nata da kyar tayi namijin kokari ta danni zuciyarta sannan ta dago dara-dara idanu ta masu masifar jifa Amar ciki yanayi na zazzafa soyayya ta tace na'am shiru Amar yayi kamar yafasa fadar abunda yayi niyar fada daga bisani ya durkusa a gabanta yace raheela bazan boye miki ba zuciya ta takasa hankuri da juriya akan sonki ina sonki raheela basan ya akayi nafada cikin soyayyar na'eema duk da na aure na'eema zuciyata takasa hankura da ke sonki a cikin jinina yake raheela na tabbata koda za'ayi nassara rabani da sonki tabbas sai an tsiyaye jini jiki na tun lokacin da yafara magana idanu raheela suke fitarda hawaye sai faman aika masa kallon tsana takeyi daga bisani tace............. Barka Ku da sallah 'yan uwa musulmi Allah ya karbi ibadamu yanuna mana badi. {Ameen} Jeeddah Aliyu🌹🌹 [11/07 8:44 am] Jeeddah Aliyu🌹: [09/07 6:29 pm] Jeeddah aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 {Part 2} 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 5⃣6⃣ Gaskiya yaa Amar kwakwalwa ka tana da matsala yanzu kai ko kunya bakaji ina matsayin 'yar uwar matarka amma kana furta mini irin wadanan kalamai, tir da wannan dabi'a taka irin ta karnuka kum...cikin zafin nama yakai mata wawa duka a baki Wanda yahadasa mata hadiye sauran kalaman ta, a harzuke yace don tsabar iskanci ni zaki danganta da karnuka"? So ba karya bane raheela ina sonki kuma har abada bazan daina sonki don haka kiyi duk abunda zaki iya banza 'yar reni hankali tsanani mamaki ne yarufe raheela sai faman zarar idanu takeyi wai yaa Amar wane irin shu'umi mutum ne?? Harara galla mata yace daina kallo na in baso ki keyi na tsiyaye miki kwayar ido da sauri ta sunkuyarda kanta tana shafar labba ta, ya mike tsaye hade da daukar plate din abinci da yakawo mata, gani zai fice da abinci yasa tayi magana cikin sarkewa halshe yaa Amar yunwa nakeji fa, a fusace yajuyo yace sai ki nemo kare da zai baki abinci ta marairaice murya tace ni dai dan Allah kayi hankuri kabani abinci naci kallon uku saura kwabo ya watsa mata daga bisani yace ae nayi tsanmani a matsayin iya shegenki zaki iya jure yunwa shiru tayi takasa furta komai saida ya dama don kanshi ajiye Mata "plate" din daga bisani yajuya yafice daga dakin raheela ta raka shi da katuwar harara tadauki plate din tafara lodawa hanji ta abinci, tana ci tana zagin Amar cikin zuciyarta ta kuma kudiri aniya ko da bala'e second semester" bazata zauna a gidansa. Amar na fita kaitsaye dakin na'eema yanufa tana kwance akan gado ta dukufa wurin nemowa kanta mafita yayi sallama yakarasa kusa da ita, a sanyaye ya kira sunanta kamar jira takeyi sai kawai tafashe da kuka da sauri Amar yadago ta ya manna ta a kirjin shi, yasoma rarrashi ta kiyi hakuri na'eema nima ba'a so raina na mare ki ba gani nayi kina kokari aikata mumuna aiki shiyasa na dauki wannan mataki amma har ciki zuciya ta banji dadi faruwa hakan ba na'eema ta share hawaye fuskarta ta zare jikinta daga nashi tace to me tazo yi a gidanan ni na tabbata zuwa raheela babu alkhairi a cikin sa domin gashinan tun ba'aje ko ina ba kafara duka na akanta don Allah yaa Amar in har da gaske kana sona kana kuma son farin cikina da kwanciyar hankali na raheela ta koma Kaduna a gobe wannan shi zai tabbatar mini da cewa babu saura son raheela a zuciyarka Wani shegen murmushi Amar yasaki duk kwarewa mai karatu da son kwan bazai iya gano me wannan murmushi na Amar yake nufi, ciki kwarewa da iya sarafa zuciyar na'eema yafara tsara ta haba my sweet na'eema ke ko ance da ke ina son wannan shashasha yarinya zaki yarda ne"?? Ae raheela "she is not my type" me zanyi da ita yarinya da Sam batada hankali ae ko daga ni sai ita mukayi saura a duniya ba abunda zanyi da ita ko yanzu da zata zauna a gidanan zata zauna ne albarkaci daddy amma ke kanki kinsan "I hate her" so kidaina tada hankalinki akan wannan kwaila yarinya tsanani ki da ita ido banaso kina shiga harkata ba ruwanki da ita a sannu zan koya mata hankali kuma daga yau matukar tana gida duk wani aiki na gidanan ita zata dinga yi ke kuma ki dinga yi min kwalliya ina kallonki ina Kara sonki ae ni 'yar aiki na kawo miki, na'eema ta kyakyale da dariya farin ciki ta qanqame Amar tace shiyasa nake matukar sonka, my hubby" Amar ya sunbace gefen wuyanta yace my na'eema yunwa nakeji mu je kibani abinci da sauri ta Mike hade da fadar yanzu yaa Amar baka ci abinci ba"?? Amar ya kashe mata ido daya yace ta yaya zan iya cin abinci gimbiya ta tana fushi da ni na'eema ta kara langwabe kai kamar qadangarwa yayida dadi yake ratsa sassa jikinta kafin tadawo da natsuwarta Amar ya sunkuce ta yanufi falon kasa da ita sai faman kyakyala dariya sukeyi suna saukowa kasa dai-dai lokacin da raheela tafito domin ta ajiye "plate" kallon daya tayi musu ta kauda fuska ta nufi "kitchen" ta ajiye plate din tafito har tayi kusan kaiwa kofar dakinta Amar ya kwada mata Kira kee raheela zo nan' Shiru tayi zuciyarta na tafarfasa domin tasan wani wulakanci ne ya shirya mata yadaka mata tsawa cikin hargowa yace ba kiranki nakeyi ba raheela takarasa wurin shi taja tayi tsaye ta kuma sunkuyarda kanta kasa saida yagama shan qamshi sa yace abunda nakeso da ke daga yau duk wani aiki na gidanan ke zakiyi tun daga kan wake-wake, shara har izuwa kan girki ke dinga yi a firgice raheela tadago idanu ta tana qare masa kallo daga bisani ta yatsine fuska hade da tabe baki Amar yace ko bakiji abunda na fada bane da kika wani tsare da ido"? Raheela ta murguda baki tace naji amma a cikin abubuwa uku nan da ka lissafa guda biyu kacal zan iya sai ka nemo wanda zai dinga yi ma guda daya, har ta dasa aya a zance ta Amar yana kallonta kafin yayi magana na'eema tayi karaf tace baki esa ba wallahi ae nan ba gidan kaka bane Inda ki ka saba zuba iya shege ki a kyale ki tun da ki ka zabi ki zauna a gida na dole ki bauta mini in kuma ba haka ba sai ki tattara shirgi ki, ki koma inda ki ka fito raheela tayi mata kallo ke a suwa dan wake a "hotel" tace yaya na'eema kenan kedai kina taqama da wannan kango wannan abin ne gida ta nuna falon da yatsanta takara yatsine fuska tacigaba da cewa ni bana kallon wannan abun a matsayin gida ke ya eshe ki na'eema ce tadaka mata tsawa ta mike tsaye da suna ta tunkuri wurin raheela tayi mata dukan akawo wuka Amar ne yataka mata birki ta hanya rike hannuta, yace tadawo ki zauna my na'eema ki barni da ita ae tafi kowa sani halina banida kyau bata tsokano ni ba na lakada mata duka ballatana tashiga gona ta kawai ki zuba ido ki sha kallon yanda zan girbe ta ya mike yanufi wajen da raheela take tsaye raheela nagani haka tafara ja da baya na'eema ta kyakyale da dariyar mugunta kafin yakaraso raheela ta kwasa da gudu tafada "bedroom" dinta ta murza key Amar yayi tsaye yana shafar sumar kanshi fuskar dauke da murmushi mtss.. Na'eema taja tsoki domin haushi Amar yabata sakamako murmushi da taga yanayi cikin zafin rai tanufi bedroom dinta Amar yabita da kallo ya tabe baki yadauki Key's din motarsa yafice daga gidan... [11/07 8:42 am] Jeeddah aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 {Part 2} 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 5⃣7⃣ Raheela na rufe kofa tayi kwanciya ta tadauko wayarta ta kira kaka, raheela naji muryar kaka tasaki ajiyar zuciya cikin shagwaba tace kaka nayi kewarki kaka tace nima haka raheela wannan boko banyi min adalci da ya nisanta ni da ke raheela tayi dariya tace to ya za'ayi kaka tunda daddy yanace akan sai nayi karatu anan kawai ki tayani da addu'a kaka tace addu'a inayi raheela saidai nakara bisa ga wance nakeyi miki Allah yayi miki albarka ya tsare min ke "ameen kaka raheela tafada hade da share hawaye fuskarta kaka tace ina fatar mutane gidan basa takura miki"?? Raheela tayi murmushi tace kaka kenan ko kwana daya banyi ba ta yaya za'a takura min"? kaka ta kyabe baki tace halin mutane gidan nasani daga maigidan har matar gidan basuda kirki duk Wanda yataba ki, ki kirani a waya ki ga yanda zan cin mutunci mutum, raheela tayi dariya tace ba Wanda zai taba ni kaka ni da nazo karatu Ina ruwa na da shiga sabgar mutane gida kawai abunda nazoyi shi zanyi, kaka tace da kyau 'yar albarka ki kula da kanki kinji"? To kaka ki gaida gida" Gida zai ji" raheela ta kashe wayarta kamar jira akeyi tagama waya da kaka "call ya shigo gani sunan da ke kai kawo bisa "screen" yahadasa mata faduwa gaba me wannan dan duniya yake nema a wurina"? mtss... Bazan dauka ba ballatana har yasami damar fada mini maganar banza yayida wayar tacigaba da "ringing" raheela ta ya mutsa fuska tamkar za ta fashe da kuka a baiyane tace gaskiya yaa Amar tsoho maye ne ko akan wane dalili zai dameni da kira"? Mtsss... Dan reni wayo kawai bara na dauka naji da wane sabon iskaci yazo min da shi danna received" a fusace tace "hellloo" Amar take kwance a falon Dr kabeer yace "what's my baby doing"? Raheela ta zaro idanu tace bansaniba, Amar yasaki mushiriki murmushi yace ina fatar ba wani laifi nayi da ya hadasawa baby naa fushi da ni"?? Saura kiris raheela ta kurma ihu domin ita yafara fin karfinta duk haka sai ta zabi hanyar zazzaga masa rashin mutunci lamba daya ko Allah zai sa ya harzuka yafita hanyarta, wai ka yaa Amar wane irin banza ne maras zuciya"? kaifa mijin 'yar uwa taa ne in har kai baka gudun abin kunya ni ina gudun sa, Amar ya zaro ido tamkar yana gaban raheela cikin zafi rai hade da konar zuciya yace raheela ni za ki kira da banza"?? Eh" na kira ka din tunda nake bantaba gani banza irin ka mai budurwa zuciya shu'umanci ka na banza ne tunda a gaba yaya na'eema bazaka iya furta mini Kalmar so wannan shi ya tabbatar mini da cewa kai nusari ne kuma duk rana da ka kuskura ka kara furta mini wannan shirme naka sai na fadawa daddy domin yanzu na fahimci kadaina tsoron kaka, mtss shashasha kawai batare da ta jira jin abunda zai fada ba ta kashe wayarta, Amar ya kurawa waya ido sai faman huci yakeyi, Dr kabeer yafito daga kitchen hannu shi rike da lemon kwali da cup's gani yanda Amar yake huci yasa ya jefa masa tambaya ta hanyar fadar kai kuma kai da wa irin wannan huci haka"?? A fusace Amar ya mika hannu bisa "stool yadauki kwali sigari ya zaro guda daya yacila mata wuta cikin konar zuciya yake zukarta yayida Dr kabeer yake aikin kallo shi, saida ya zuke sigari tass ya jefa "filter cikin ashtray" yadafe kanshi hade da sauke ajiyar zuciya, Dr kabeer yakara jefa masa tambaya wai meke faruwa ne da wa ka ke waya ne"?? Cikin sanyi murya Amar yace raheela ce kb da raheela nake waya me nayiwa raheela ta tsaneni"?? Cikin dinbi mamaki Dr kabeer yafurta sunanta raheela cabdijam dama har yanzu Amar son raheela yana tare da kai"?? Amar ya yatsine fuska yace kwarai kuwa kb har gobe ina son raheela" Amma kasan wannan kuskure ne koh"? I known kb but nima bansan me ke damu na zuciyata tazamo bana iya sarafa ta itace take sarafa ni wasu lokuta zan ji na tsani raheela tsana mai tsanani gaske a wani lokacin kuma sai naji duk duniya ba mace da nakeso irin ta I don't known what's wrong with me" Amar yakarasa zance sa hawaye suka wanke masa fuska abinda yakara jefa Dr kabeer cikin firgici kenan da sauri ya zauna kusa da Amar cikin sigar rarrashi yace kadaina kuka Amar nasan daci da zafi da so yakeda shi, amma na tambaye ka mana"? Amar yadaga masa kai, Dr kabeer yacigaba da cewa Amar kadaina son na'eema ne sannan kuma kanada labari cewa babu aure tsakani ka da raheela"?? Amar yasaki ajiyar zuciya hade cewa kb ina matukar son na'eema babu abunda ya sauya daga dinbi soyayya da nakeyi mata, ina sane da cewa raheela ta haramta a gareni ae ni ba jahili bane nasan abunda nakeyi" Harara Dr kabeer ya watsa masa cikin baci rai yace in har kai ba jahili bane to kai kursugumi dan iska ne tayaya zaka bari shedan yayi tasiri a zuciyarka ka hade soyayya'r ya da qanwa wannan ae ganganci ne kayi kokari ka rarrashi zuciyarka ta hakura da soyayya raheela gudun tafka abin kunya. Har Dr kabeer yadasa aya a sharhi sa Amar yana kallon shi saida ya share tsawon dakika biyar yana kallon Dr kabeer daga bisani yace bazan iya daina son raheela saboda son ta yariga yazame mini jini jiki na kawai zanyi kokari nadanne duk wani " feeling's da nakeji akanta koda hakan yanufi ni zan rasa nawa kwanciyar hankali zan tattara duk wata soyayya da nake yiwa raheela nadawo mata yaa Amar din da tasani a bayan zan dawo mata mugu maras tausayi amma ba wai don na daina sonta ba. Mtss... Dr kabeer yaja tsoki hade da cewa chan ta matsi maka ita dai bata kallo ka a matsayin masoyi saidai Mijin 'yar uwar taa don haka iska ne kawai yake wahalarda mai kayan kara" Amar yayi miqa hade da cewa kb kenan bakasan so bane shiyasa amma da kasan dadi da radadi so da ka tausaya min Kb ya tabe baki yace "please mu ajiye zance raheela a gefe mu yi zance da ke gaban mu. Ta bangare raheela kuma tana ajiye waya tafashe da kuka tafara zance zuci na Shiga uku ni raheela wannan wace irin masifa ce yaa Amar yake yunkuri jefa ni a ciki"?? Takara fashewa da kuka cikin shashekar kuka tafara magana kamar wata zarara wallahi na tsane ka yaa Amar kuma har abada bazan taba sonka, tsanani na da kai kiyayya ce kuma duk ranarda ka kara furta mini kalma son sai na fadawa daddy" koda hakan yana nufi zai tarwatsa zumuncin iyayye mu haka raheela tacigaba da tsoki burutsu ta ita kadai. ********************* WASHE GARI**** Da misali karfe 10:30am Amar da na'eema suna zaune bisa "dining table" suna breakfast" cikin rashin walwala Amar yajuya wurin na'eema yace ki shirya za mu fita" Na'eema tace hubby ka manta yau Sunday"?? Amar ya galla mata harara yace yau Sunday ni chiristan ne da za ki tuna mini yau sunday kinga malama in kinada ra'ayi fita "fine in kuma bakida karki fada mini maganar banza yana karasa magana ya Mike cikin zafin rai har yana ture kujera yanufi falo yabar na'eema cikin mamaki dalilin wannan daukar zafin dole ta mike tashiga bedroom tadauko mayafi da handbag dinta Amar yajuya tabi bayansa yayida raheela da ke dakin ta taji karar tashin mota da sauri ta leqa window" tayi murmushi jin dadi tace umma ta gaida ayshat jarababu kawai kalli fuskoki su a murtuke kamar Wanda aka aikowa sakon mutuwa nima yau zan sake nayi yanda nakeso ba mai takura ni raheela ta kyakyale da dariya mugunta tace za Ku gane kuskure Ku na bari na a gidanku don sai nayi muku barna da zata hadasa yaa Amar ya mayarda ni Kaduna da sauri ta nufi falon tasoma karewa falon kallo tana tunani da me zata fara........ Jeeddah Aliyu🌹🌹 [14/07 8:52 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [14/07 8:13 am] Jeeddah aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 5⃣8⃣ Kaitsaye tadoshi kitchen ta bude dif freezer" ta zaro idanu tace cabdi aikin wani sai kallo, kalli yanda yaa Amar yacika freezer da naman kaji sai kace bai Sam zafin kudi ba ae kuwa nima yau zan wasa hakora na ta kyakyale da dariyar mugunta taciro kaji har gudu uku ta ajiye su huce tajuya tanufi dining area" ta budi Warmer's din ke ajiye bisa table tabe baki tayi hade da yatsine fuska ta dauki " fork" tasoma cin chip's tana yatsine saida taci Mai esarta ta ajiye fork tadaga warmer tajuye saura chip's din a kasa takara bude wata dayan warmer farfesu ne a ciki da sauri ta kauda fuskarta tasoma bin kowane sako da lungu na dining tana zubarda shi tagangaro har zuwa falo ko ina saida tayayafa masa miyar farfesu tanayi tana kyakyale dariya tana kamallawa tayi jifa da warmer tayi tsalle ta bugi stool ta tsage takara kwashewa da dariya tanufi "fridge" tana budewa ta washe hakora sakamako gani robobi "ice cream birjik ta kwaso manya-manya robobi har guda hudu tace na sha biyu na zubarda biyu ta nemi kujera ta hakince sai kace itace na'eema da kyar tashanye guda daya tabi saura uku din tadinga shafawa "tile's" sai da takarar da shi tass sannan tajefarda "empty roba ta koma kitchen tadaura tafasa kajinta tadawo falo ta kunna kallo tanayi tana addua'ar kada Allah yasa masu gidan su dawo da wuri sai tagama shagalin ta, har raheela ta soye kajin'ta tass Amar da na'eema basu dawo ba mangyada da tayi amfani da shi tajuye shi a kasan tile's din "kitchen" ta kinkime warmer" da ta zuba kajinta takai daki, tun daga kitchen, dining har izuwa falo sai da raheela ta hargitsa su sannan tanufi dakinta ta murza key ta kwaso "lollipop" ta haye gado tayi kwanciyar'ta, tana tsotsan lollipop tana murmushi domin tasan ba karamar ta'asa ta yiwa na'eema sai misali kar'fe 5:30pm Amar da na'eema suka dawo gida suna jefa kafafu a falon suka ja birki sakamako gani yanda falon'su yadawo tamkar na mahaukata, na'eema ta kalli yaa Amar cikin rawar murya tace yaa Amar kana kallo abunda raheela ta aikata koh"? Amar yayi shiru kamar baiji abunda na'eema tafada, ba gani yadda yayi shiru batare da yace komai ba yasa tacigaba da fada wannan wulaqanci da me yayi kama"? Ina zamana cikin kwaciyar hankali kaje kadauko mini annoba in kai za ka iya cigaba da jure iya shegen'ta ni ba zan iya ba dole raheela ta tattara kayan'ta tabarmin gidana, tun daga lokacin da raheela ta jefa kafar'ta a gidanan zuciyata take bugawa na nemi natsuwa da kwanciyar hankali'na narasa akan wane dalili zan cigaba da zama da ita lalle kanada bukatar zabi tsanani ni da ita dole ka zabi daya tana karasa zance tajuya, tanufi "bedroom" d'inta karaf idanu ta suka hasko mata kofar "kitchen" a bude kawai sai tafasa shiga dakin tanufi "kitchen" tana jefa kafar'ta tsantsi mangyada da ke zube a kasa ya kwashe ta sai akayi sama da ita aka yarbe ta kanta ya bugi "cabinet" tasaki razananiya qara da sauri Amar yanufi kitchen d'in na'eema nayi masa nuni da hannu wai kada yashigo Sam Amar bai fahimci inda ta dosa ba ae kuwa yana jefa kafar'sa dama gashi sanye da "cover shoe" da karfi tsantsi ya kwashe shi bai fadi a ko ina ba sai bisa ga na'eema kanta yaqara bugu "_tile's" da kyar Amar ya iya mikewa tsaye, ya taimakawa na'eema ta mike kowane su kayan jikin shi yadebi mangyada suna kaiwa falo Amar yasaki hannuta cikin tsanani zafin rai da konar zuciya yanufi bedroom d'in raheela yana murda "handle yaji kofar a rufe cikin yanayi na Wanda zuciyarsa take tafarfasa yafara dukan kofar hade da kiran sunan'ta..... [14/07 4:08 pm] Jeeddah aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 5⃣9⃣ Raheela na jin sa tayi biris da shi sai ma tacigaba da tsotsan "lollipop dinta Amar yakara harzuka yace na rantsi raheela in baki bude kofar nan ba in na kamaki sai nayi miki illah. Raheela ta tsintsire da dariya ta sauko daga bisa gado tanufi bakin kofa ta rami "key ta leka tace yaa Amar kanaji na kuwa"? Da sauri Amar yace ki bude kofa nace, raheela ta galla masa bazawara harara kamar tana gani sa tacigaba da cewa in kana yiwa Allah" yaa Amar in ka kamani karka barni da raina ka yanka ni. Amar yakara hasala sai cika yake yana batsiwa raheela ta kyakyale da dariya daga bisani tace da wannan huci da ka keyi dama zuwa kayi kataya matarka aikin gyara barna da nayi, Amar ya girgiza kai yayi kyaci yajuya ya koma falo tarar'da na'eema tana shara yaja tsoki yanuna ta da yatsa yace duk laifi ki ne na'eema, a fusace na'eema tace da nayi me"? Sai da ya watsa,mata harara sannan yace da ki ka hana akawo miki 'yar aiki kin dauki baqin kishi kin azawa kan'ki sai kace ke kadai ce mai miji" Tsanani baci'n rai yarufe na'eema tace tuni na fahimce ka mayarda ni juji duk lokacin da ka debo shara akaina ka ke juyewa, in har raheela tafi karfin'ka bazaka iya daukar mataki akanta, ni zan iya domin duk ranar'da takara kwatata mini wannan dabbaci a gida sai na karya ta. Amar yayi murmushi domin yasan burga ce kawai irin ta na'eema ko jiya da taki raheela, ta zauna lafiya sa'a ce ta taka, shi kanshi yayi mamaki yadda raheela takasa ramawa, ya tabe baki batare ya tamka mata ba ya haura sama yayida na'eema ta bishi da mugun kallo. A WASHE GARI****** Amar yakai raheela school saida ya tabbatarda ta zama cikkaka daliba sannan yanufi "hospital" ranar farko da raheela tafara zuwa "school" tayi qawa mai suna Ayshat kabeer, "course" din su daya wannan yasa suka shaqu cikin dan kankani lokacin, duk fadi garin abuja raheela batada qawa in ba Ayshat ba, duk da kasancewar Ayshat ta girmewa raheela kuma gata matar aure amma a hakan suke qawance su. Raheela tadawo daga "school" ga gajiya ga kuma yunwa da ta kwaso da yake Ayshat ce ta mayarda ita gida ta balle murfi mota tafito a kasalace tace besty sai gobe in mu hadu, ayshat tayi murmushi tace ke dai kinshiga uku besty Sam bakya da hankuri yunwa, raheela ta ya mutsa fuska tace inada gaskiya ayshat yunwa ba'a bar hankuri bace nantake zata yiwa mutum illah ayshat ta kyakyale da dariya taja motar ta tayi gaba, yayida raheela ta bude kofa tashiga cikin gida Joseph da driver umma hajara na zaune a baki gate" drivern na gani raheela yafara washe hakora wanake gani kamar dan audu"?? Nine raheela mu same Ku lafiya"? Lafiya qlau dan audu kai da wa ka zo ne"? Umma hajara ce na kawo, ido raheela ta zaro tace umma hajara fa"? "Eh dan audu yafada yana kallo fuskar raheela" Yayi kasa da murya yace inaso nayi wata magana da ke raheela amma dan Allah ta kasance sirri a tsakani mu raheela tayi shiru tana kallon sa daga bisani tace inajinka dan audu' A haqiqani gaskiya raheela yau na tsorata da abunda kunnuwa na suka jiyo mini, kamar yadda nasaba kai hajiya hajara wani kauye da ke Niger state wajen bokanta yau ma hakan ce ta kasance baya nayi mata rakiya a bakin kofar gidan bokan har na juya sai na tsince kaina da son jin abunda yakawo ta wajen bokan sai na labe, kamar daga sama naji tace boka duguzuu so nakeyi raheela ta mutu ko ta haukace domin tana daf da ta rusa rayuwar 'yata, tun lokacin da dan audu yafara magana raheela ta shiga firgici hade da rudani ta nemi natsuwarta tarasa sai gumi yake fita daga sasssa jikinta....... Jeeddah Aliyu🌹 [20/07 7:23 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [20/07 3:50 pm] Jeeddah aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 6⃣1⃣ Cikin rawar murya raheela tace laifi me na yiwa umma da take yunkuri gani bayana"? Ni ma bansaniba raheela amma duk abunda nafada miki babu ,karya ko kazafi a cikin'sa domin ina da sheda Mai karfin gaske ba ma shi kadai ba har asiri ta karbo Wanda zai yi sanadi da Amar zai manta da ke da iyayye sa tabbas hajiya hajara batada imani domin asiri da boka yabata Wanda za ki haukace ko ki mutu cewa yayi ta nemi Sabon kabari ta binne asiri a ciki za ki mutu in kuma ta binne a tsohon kabari za ki haukace, na rantsi raheela bantaba shiga tashin hankali da firgici irin na jiya, da sauri na bar jikin bukka da na labe na nufi kofar gida, bayan kamar mintuna biyar da fitowa ta, sai ga ta tafito muka nufi Inda nasaba parking d'in mota bayan mu dauki hanyar dawowa garin Kaduna sai take cewa da ni dan audu akwai wani aiki da zan baka zan kuma baka naira dubu hamsi da ina fatar baza'a samu matsala ba domin nasan za ka iya. Har ta dasa aya a zance ta zuciya ta, tana buguwa da karfi domin na tsorata da lamari ta, nace bakida matsala hajiya amma wane irin aiki ne"? Kaitsaye tace da ni wannan abun nakeso ka binne mini shi cikin sabon kabari kuma banaso a sami kuskure, karka sake kasaka a tsohon kabari a sabo za ka binne, nace to hajiya angama na mika hannu tabani asirin, har mu ka eso gida ina tunani ta yadda zanyi na kubutarda ke daga wannan halaka saboda na fahimci bataso ki haukace tafiso ki mutu, wallahi raheela daren jiya banyi bacci ba sai kuma gashi yau tace na kawota abuja, wannan ya tabbata min da cewa za ta kawo wa na'eema asiri ne, tasakawa Amar cikin abinci, hannu shi ya zura cikin aljihu rigar shadda da ke jikinsa yaciro wata 'yar batta mai lullube da fatar kura ya mikawa raheela, jikinta na rawa ta amsa yayida dan audu yacigaba da cewa wannan shine baqin asiri da akayi miki yanzu kuma sai kiyi kokari ki ruguza Wanda aka yiwa Amar tasaki ajiyar zuciya daga bisani tace, na gode dan audu insha Allah zan yi iya kokari na nagani hakar' su bata cima ruwa ba, dan audu yace ba komai raheela ae yiwa kaine ki yi maza ki shiga gida kada tsatsayi yasa tafito tagani tare da ke ae kuwa da sauri raheela ta nufi cikin gida har tayi niyar ta bude kofar falo tashiga sai kuma tafasa ta bi kofar baya wance ake shiga falon Amar tasoma sanda kamar barauniya ta leqa falo na'eema saida taga wayam alamar basa cikin falon suna "bedroom" da sauri tanufi " window" dakin na'eema ta leqa na'eema da umma hajara na zaune bisa gado sai faman zuba sukeyi muryar umma ce ke tashi ki tabbata ki zuba masa magani nan domin dan asarariya ya tabbatar mini cewa matukar Amar yaci magani nan hatta da uwar da ta haife sa zai manta da ita, ballatana wata raheela banza, bazara na'eema tasaki murmushin jin dadi tace karki ji komai umma naa yau d'inan zan cika aiki, umma hajara ta Mike hade da daukar "handbag" d'inta tace ni zan wuce banaso Amar ya dawo yatararda ni gidanan, na'eema tace to umma mu je na rakaki, da sauri raheela tashige cikin labule ta boye saida taga fitar su sannan tafada dakin na'eema tasaki katuwar ajiyar zuciya sakamako gani leda baqa bisa "dressing mirror" hannuta na rawa tadauke leda d'in tafice dakin da sauri ta bi kofar da tashigo tafita tana kallo driver yaja mota suka fice daga gidan akan idon'ta na'eema tashiga gida saida ta dauki tsawon dakika biyar sannan tashiga cikin falo tayi sallama mtsss na'eema taja tsoki hade da watsawa raheela kallon banza daga bisani ta kyakyale da dariya cike da nishadi ta haura sama, yayida raheela ta bita da kallo a zuciyata tace "Allah zai kareni daga sharri Ku. Tun lokacin da raheela tashiga daki take kwance duk yunwa da takeji nemanta tayi ta rasa, sai faman tunani mafita takeyi nan take Ayshat kabeer tafado mata a rai tabbas Ayshat ce zata warware mini wannan matsala. [20/07 7:22 pm] Jeeddah aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 6⃣2⃣ Domin banida wata abokiyar shawara duk fadin garin abuja da yawuce ta, ya zame mini dole na kwancewa ayshat wannan sarqaqiya ko zan sami mafita. Tabangare na'eema kuma bata qara tunawa da wani zance magani ba, saida ta kamalla girki ta dare da gudu tafada " bedroom" d'inta saidai kash domin duk Inda take tsanmani zata ganshi ta nema tarasa taja dogon tsaki mai cike da jin haushi a baiyane, tace ba komai don wannan yabata ba komai bane dama raheela ce babbar matsalata kuma dan audu, yace yacika aiki akanta cike da gamsuwa tajuya ta koma "kitchen" Tun lokacin da raheela tashige d'aki bata qara fitowa ba, har akayi sallah magarib da esha'i tana d'aki zamanta. Amar da na'eema na zaune a falo Amar kasa hankuri saida yafurta abinda ke ci masa tuwo a kwarya ta hanyar cewa, na'eema yarinya nan lafiya take, nasaba dawowa daga "office na tararda ita zaune a falon nan sabani yau ko motsinta banji ba"? Na'eema ta yatsine fuska tace, oho ni bansaniba, sai kaje ka duba in tana raye" Tsantsan mamaki ya baiyana akan fuskar Amar yace "what's nonsense" na'eema me ki ke nufi da wannan banzan magana naki"? "Look yaa Amar karka dameni da maganar raheela domin ita da babu duk daya suke a wurina, kai da kadamu da rashinta sai kaje ka dubata domin d'akin nata ba bako ka bane. Amar ya mike tsaye batare da ya tankawa na'eema ba yanufi d'akin raheela, yayida na'eema ta bishi da harara a zuciyata tace munafuki gawa za ka tarar domin,na tabbata raheela ta zama tarihi yanda take da dan banza ci kamar gara ace har yanzu bata fito ta narki abinci ba lalle aikin duguzuu yayi ba qarya tadauki "remote control" taqara "volume" d'in tv domin bataso Amar ya kwada mata kira in yatarar da gawa raheela shine taqure "volume" ya murda "handle ya ji kofar a rufe sai kawai yafara "knocking" raheela da ke kwance tana "game" a wayarta ta yatsine fuska hade da cewa waye anan"? Amar yace maigida ne sai ki zo ki bude masa kofa koh"? Raheela tayi murmushi a zuciyata tace, hero sarkin rigima yau kuma ta wace rigima ya zo min da ita oho" Ta Mike kanta ba dan kwali jela gashi ta na reto, ta murza "key kofar ta bude sai ga Amar tsaye hannaye shi zube cikin aljihu wando "jeans d'in da yake sanye da shi, raheela ta bata fuska cikin gatsi tace ya akayi ne maigida"? Batare da yabata amsa ba yasanya hannu shi daya ya tureta, yaqarasa shiga d'akin, raheela ta tabe baki samako gani yanda yake kallon d'akin nata, batare da ya kalle ta ba yanuna "bedside" da yatsan sa yace ke yanzu don tsabar kwarewa da qazanta shine da ki kayi ciye-ciye ki sai ki ka zubarda ledoji biscuit da lollipop" a gefen gadon ki saboda bakisan hanyar "dustbin" ba koh"? Saida ta dan Sosa gashin kanta ta wani yatsine fuska tace zuwa, kayi ka duba lafiya ta a matsayinka na Wanda aka bawa amanata ko kuma zuwa kayi ka duba yanayi tsaftar d'akina a matsayinka na malamin kuda"? Murmushi yasaki daga bisani yace "anyway" mu ajiye wannan zance a gefe miyasa yau banganki a falon ba"? Banyi ra'ayi bane datz why bakaganni ba, so akwai matsala ne"? "Nop" amma yakamata kifito ki ci abinci koh"? Raheela ta zaro ido hade da dafe kirji kamar wance taga abin tsoro, daga bisani tace na koshi' Amar ya tabe baki yajuya yafice daga d'aki yana Shiga falon yadauki remote" yarage "volume" ya gallawa na'eema harara yace nan ba cinema" bane da za ki cikawa mutane kunne da hayaniya, na'eema ta tabe baki tace bani ce na kai zomo ba rataya aka bani, mtss.. Amar yaja tsoki ya haura sama yabar na'eema cikin yanayi na qila wa qala nan take tafara zance zuci, nashiga uku ni na'eema bani bajin dadi rayuwar aure matukar raheela na numfashi, ki taimake ni raheela ki mutu ko nima zan samu na mallaki zuciyar yaa Amar gani wannan tsoki burutsu ba zai fisheta ba ta mike tanufi bedroom d'inta. A WASHE GARI******* Amar yasauke raheela a "school" kaitsaye tanufi "department" d'insu tun daga nesa ta hango ayshat da wasu course mate" d'insu a zaune kallo daya ayshat tayi mata tagano tana cikin damuwa domin bata saba gani ta cikin irin wannan yanayi, ba ta Mike tsan tariko hannu raheela tace zo mu je mota besty na baki saqo ki, ayshat ta bude mota suka Shiga tace lafiya raheela me ke faruwa naganki haka"? Raheela tasauke ajiyar zuciya yafi a kirga daga bisani tace.... Masoya littafi mijin 'yar uwa taa banida lafiya shiyasa kwana biyu Ku kadaina gani new post😭 Jeeddah Aliyu🌹 [21/07 10:02 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [21/07 10:16 am] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 6⃣3⃣ Ayshat ina ciki tsanani damuwa hade da neman mafita nan take raheela ta kwararo mata, tarihi rayuwata har ta gangaro a labari abunda yafaru jiya, ta kuma zuge zip d'in "handbag" d'inta ta fito da batta da dan audu yabata, taqara dauko garin magani da tadauko a d'akin na'eema ta mikawa ayshat cikin sanyi murya tace ayshat bansan ya zanyi da wadanan abubuwa ba saboda ni har tsoro suke bani, ada nayi tunani ko na fadawa kaka sai kuma na ga zan qara tsokano wata masifa ne wance tafi wannan shiyasa nazo gareki ayshat ko kinsan yadda za mu yi "destroy" d'in su"? Tun lokacin da raheela tafara magana ayshat take kada kai tasaki ajiyar zuciya mai karfi gaske, daga bisani tace amma a duniya ina gani marasa imani da tausayi bantaba cin karo da irin umma hajara da 'yarta, wannan ae jahilci ne a tunani yanzu ko a kauye andaina hulda da bokaye domin yanzu kai yawaye ilimin addini ya yawaita a ko ina, mutane sun gano cewa bokaye da malamai tsinbu mak'aryata ne ashe ba haka bane har yanzu da sauran baragurbi a cikin al'umma to Allah yashirye su yaganarda da su gaskiya, domin shi lamari na ubangiji ba'ayi masa shishigi, in Allah yayi ke matar Amar ce sai kashe na'eema ki aure Amar shikenan dole umma hajara ta rungumi kaddara domin haka "Allah {s,w,t} yanufa kuma duk tsabar kiyayya da takeyi miki bata esa ta kashe aure ta da abbanki ta maye gurbin na'eema a gidan Amar, kinga kenan haukar banza ce takeyi da kuma karanci ilimin addini da ke damunta domin na tabbata da umma hajara tanada wadace ilimin wannan jahilci duk bazata aikata shi, ba ita kuma na'eema so ne yake yunkuri kaita mahalaka ki zuba ido raheela nan bada dadewa ba, za ki ga asiri su ya tonu domin da gani wannan aure na Amar da na'eema bana "Allah da Annabi bane akwai wata a kasa. Raheela ta goge gumi da ya karyo mata da gefe mayafinta, tace duk wannan abu da yaya na'eema da umma sukeyi sunayi sa ne abisa rashin sani suna daukawa Kansu zunubi a banza, ni da Duke yiwa asiri bantaba son yaa Amar ba asalima bantaba tsanar wata halitta irin yadda na tsane shi, kuma na tabbata shima babu sona ko misqarazati a zuciyarsa, yayi amfani da kalma ne kawai don yarusa shakuwa da kauna da ke tsakanina da yaya na'eema kuma yayi nasara, duk haka yaa Amar bai fasa dangantani da mumuna kalamansa na soyayya ko yana tsanmani karamar kwakwalwa ce da ni irin ta shi Ayshat ta yi murmushi tace raheela kenan har yanzu kurciya na damu ki, raheela ta tabe baki tace 13yrs ne da ni ayshat ta kyakyale da dariya hade da cewa naga alama raheela ta balle murfi mota tafita, ayshat ta mara mata tana tsokanar ta gaskiya besty labari soyayya ki da yaa Amar yajefani cikin wani shauki, raheela taja birki ta kwada mata harara hade da cewa banaso iskanci besty wallahi zan b'ata da ke da sauri ayshat tariko ta tana dariya tace "Allah yahuci zuciyarki 'yar gidan kaka, raheela ta kyakyale da dariya tace Allah sarki kaka nayi "missing d'in ki. Bayan raheela da ayshat sun gama daukar "lectures" kaitsaye suka nufi gidan ayshat, da ke kado" ayshat tadauko ashana suka fito a compound" d'in gidan ayshat tayi addu'a sannan ta warware fatar kura da ke lullube da jikin batta duk wani asiri da ke cikinta saida tafito da shi ta kuma zazzage garin magani ta hade su wuri daya ta cina musu wuta, suna kamawa da wuta wata baqar walkiya tafito daga cikin wutar ta, tashi sama da sauri raheela ta qanqame ayshat, jikinta sai faman mazari yakeyi ayshat ta tureta tace dan dallah malama sakeni matsoraciya kawai, raheela tasauke ajiyar zuciya cikin rawar murya tace ayshat baki ga wata baqar walkiya ta tashi daga cikin wuta nan ba"? Na gani mana ke wannan ba komai bane kadan daga cikin aikin tsafi kenan, raheela tace cabdijam masu iya magana sunyi gaskiya da sukace tsafi gaskiyar mai shi ayshat ta kada kai hade da cewa Allah yasa mu fi karfi zuciyar mu" Ameen raheela tafada a kasalance mu je ciki in da akwai abin tabawa na cika tumbi na jiya kwata-kwata bayan biscuit da lollipop" ba abunda na ci Ayshat ta kyakyale da dariya tace wuya tasaka yarinya yin azumin dare..... [21/07 2:35 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 6⃣4⃣ BAYAN KWANA BIYU***** Na'eema ta zuba ido taga raheela ta mutu ta ji shiru gashi yau kusan kwana biyu da binne asirin amma raheela ko ciwo kai batayi ba, ta kira umma tafada har yanzu raheela na nan cikin k'oshin lafiya da budar baki umma sai cewa tayi ki qara hakuri na'eema ae nesa ta zo kusa ba dan audu ya binne asiri ba kawai ki shantake ki baza idanu ki, kisha kallo ina da yaqini aikin dan asarariya zai yi mata mumuna kamu kinsan lamari na kisa a hankali yake fara aiki in yanzu ta mutu farat daya, sai anyi bincike dalilin mutuwarta watakila kece mutum ta farko da za'a fara tuhuma domin a gidan ki take zaune amma indan ciwo yakamata sannu-sannu ana jinyarta sai ta mutu shikenan yarinya ki ci kare ki babu banbaka ba dan banza da ya esa yatuhume ki, na'eema ta kyakyale da dariya jin dadi tace da kyau umma dadi na da ke akwai "brain" kina kawo "light" Allah yabarmi ke umma naa naji dadi shinfida mulki a gidan Dr Amar matawalle "Ameen" 'yar nan. Da wannan bahaguwa shawara ta umma hajara, na'eema ta dogara. Yau Sam raheela bataji dadi zuwa "school" ba sakamako rashin gani ayshat, ae kuwa nan take ta kira ta a waya taji dalilin rashin zuwanta school ayshat tayi "picking" tace "hello besty" Raheela tace na'am gani nashigo "school banganki ba ina fatar lafiya ce ta boye ki"? Lafiya qalau bash ne yakawo min ziyara bazata, kuma yau zai koma shiyasa nayi zama na domin yana bukata ta a kusa da shi" Mtss...raheela taja tsoki tace me bash ya zo dauka a wurinki, ba sai weekend yake zuwa ba"? Bara na bashi "phone sai yafada miki abunda ya zo d'auka waka a bakin mai ita tafi dadi sauraro' Da sauri raheela tace sai anjima ta kashe waya. A lokacin da raheela tagama d'aukar "lecture" dole tanufi gate domin samu taxi da zai kaita gida dama yaa Amar ke kawota ayshat ta mayarda ita duk "taxi" d'in da ta tara taji an zafga mata kudi tace malam tafiyar'ka mtsss....taja tsoki hade cewa duk 'yan "taxi abuja barayi ne me za'ayi da irin wannan garin mutane sai 'yar banza tsadar rayuwa, tana wannan zance wata mota ta tsaya a gabanta da sauri ta kauda fuskarta mai mota yasauke "glass" ya leqo fuskarsa yace kanwata daina kawarda fuska yaya ki ne har yanzu baki sami "taxi bane"? Sai lokacin raheela tasaki fuska hada dan gajere murmushi domin tagano course mate d'inta ne Amar Ibrahim dalilin da yasa take kirasa da yaya naa kenan tace "eh duk wance na tsayar sai naganta da mutane {ni kuma 'yar gidan Shehu aliyu saura kiris dariya ta kunbuce min nace kutt su raheela an fara qarya} Ayya to shigo na sauke ki mana, saida ta yatsine fuska daga bisani tace lah...yaya naa da kabarshi da sauri yace kedai shigo tsayuwa a titi ba dadi a zuciyar raheela tace da na bada wadanan manya kudi a kaini gida gwada nashiga "lift" ta balle murfi mota tashige hade da cewa na gode yaya naa Amar Ibrahim yayi murmushi yace "you are welcome" yana yin "parking" a kofar gida raheela ta bude kofa tafito ta dan leqa kanta cikin motar tana qara yi masa godiya sai ga motar yaa Amar ta danno kai, rass...gaban raheela yafadi sai kawai ta dake kamar bata ganshi ba yadanna "horn" Joseph ya bude masa "gate" Amar Ibrahim yaja motar sa yaqara gaba yayida raheela tayi tsayin ta a bakin gate saida ta share tsawon dakika biyar a tsaye daga bisani tashiga gida, karaf idanu ta suka sauka bisa fuskar yaa Amar da ke tsaye a "parking space" sai faman kallon agogo yakeyi hade da girgiza kafa kallo daya raheela tayi masa ta kawarda fuska a baiyane kuma sai tace "poor guy" da alama matar'sa tafita bada izzini shi ba sai ta wani tabe baki tace "very sad" amma kuma na tausaya mata domin yanda naga hero yana girgiza kafa na tabbata yau zuciyar 'yan maza a bace take kamar ance taqara juyawa sai kawai ya yafito ta da hannu zaro ido tayi ta nuna kirjinta da yatsa alamar da ita yake kuwa yadaga kai ya kuma daga yatsu sa uku, raheela taqara zare ido tace wallahi da ni yake gashi nan yace kafin ya kirga uku na zo cabdijam matukar "guy" nan yadake ni akwai bala'e a gidanan don sai nafasa masa gilashi mota, gani ya lankwashe yatsu sa biyu yadaga guda daya yasa ta kwasa da gudu takarasa wurin shi, ta ja tayi tsaye ta wani turo baki hade cewa gaskiya ni yaa Amar kadaina yi min kirge da" da yanzu ba daya ba "I'm mature" so take note" Amar yayi shiru yana wasa da key d'in hannu shi, kamar baiji abunda tafada ba gani yanda ya yi banza da ita yasa ta bude "handbag" taciro "lollipop" ta nunawa Amar hade da daga masa gira tace makami kasan mu bama yawo babu makami sai kuma ta zaro ido tace kai ba fa bindiga nake nufi ba ina nufi "lollipop" naga har ka tsorata tabare abarta ta jefa baki tana tsotsa tana lumshe idanu daga bisani tace Allah yayi yiwa "company" wannan alawa albarka domin alawa ce mai kawarda bacin rai, duk lokacin da nake tsotsa ta sai na tsinci kaina cikin nishadi da annashuwa, tun lokacin da tafara zuba Amar yake mata kallon kasan ido, gani har izuwa yanzu baiyi magana ba yasa ta tabe baki tace ga shawara yaa Amar me zai hana ka bude "company" lollipop saboda na fahimci cewa kai mutum ne mai zafin rai sam bakada fara'a dariya wuya takeyi maka shiyasa ko kayi dariya baka kyau kana bude company lollipop za ka dawo kamar gonar auduga saboda, fara'a sai yaya na'eema tagaji da gani dariyar ka, takarasa zance ta tana washe hakora ita a dole so take taqara harzuqa shi. Ya lashe labba sa hade da cizo su, ya bude mota yaciro "briefcase" yace karbi ki shiga min da ita cikin gida ki cewa na'eema na koma hospital" akwai abunda na manta da zan je na dauko. Raheela ta kyakyale da dariya tace..... Jeeddah Aliyu🌹 [23/07 4:30 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [23/07 3:08 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 6⃣7⃣ BAYAN SATI BIYU****** Raheela na kwance a bedroom d'inta wayar ta yayi "ringing" ta yatsine fuska tayi "picking" kasalance tace "hello" jin muryar da batayi zato ba yasa ta mik'e zaune tace yaya hafsat saukar yaushe"? a bangare daya aka amsa da cewa jiya da yamma Amar bai fada miki nadawo ba"? Tak'ara yatsine fuska hade da cewa wannan uban 'yan miskilaci ne zai fada mini kin dawo ae ba zai fada ba, yaya hafsat tayi dariya tace yaushe za ki zo gida na"? Cikin zumudi raheela tace gobe daga "school" zan wuce gidanki, da an kwana biyu zan tattaro shirgi na nadawo gidanki da zama ni dama zaman gidanan ya eshe ni gida sai kace "prison" Yaya hafsat ta kyakyale da dariya daga bisani tace raheela 'yan mata kaka har yanzu baki daina rigima ba koh"? Nadaina yaya hafsat saidai in an tsokano ni, nakan d'an taba kad'an' Dariya yaya hafsat tayi sosai daga bisani tace sai kin zo ta kashe waya. Wani, wawan tsalle raheela tadaka a tsakiyar gado tace karshen zama na gidanan, yazo fuskar ta dauke da farin ciki tanufi "kitchen" tun kafin takarasa shiga kitchen d'in ta tsakayi na'eema ciki, har tayi niyar ta koma falon ta jira har tafito sannan tashiga sai kuma ta tuna da irin matsanaciya yunwa da takeji kawai, sai tafada kitchen d'in. Jin motsi mutum yasa na'eema ta juyo gani raheela ce sai wani yatsine fuska kamar taga kashi, cikin rashin damuwa da irin kallon da takeyi mata tanufi locker ta bude tafito da kwalin comflask" karaf idanu na'eema suka sauka bisa d'an yatsata da hamzari ta rik'o hannu raheela a firgici raheela take kallon ta a tunani ta ko za ta zanga mata mari ne domin yadda ta danke hannu nata, cikin kad'uwa na'eema tace raheela ina ki ka sami wannan zobe"? Raheela tasaki ajiyar zuciya saboda batayi tsanmani wannan ne dalilin da yasa na'eema tayi mata wannan mahaukaci rik'o ta fisge hannuta da k'arfi tace dallah malama sakeni, don kinga zobe a hannu na "so what's" A fusace na'eema tace dole na tambaye ki inda ki ka sami da wannan zobe domin na mijina ne' Hmm..su miji manya to mijin naki ne yabani Na'eema tayi shiru zuciyata na tafarfasa jin takeyi kamar tadauki wuk'a ta dabawa raheela a k'aho zuciya, tana tsaye har raheela tagama abunda ta zo yi a "kitchen" tayi tafiyarta, tabarta tsaye tana jinyar dafi da tasake mata tamkar kazar da kwai yafashewa a ciki haka na'eema taja kafafuta tafita daga kitchen d'in tanufi d'akinta. A WASHE GARI****** Daga "school" raheela ta zarce gidan hafsat ta shantak'e tayi zamanta har 10:00pm ta buga raheela tafito daga bedroom d'in yaya hafsat hannuta dauke da karamar 'yar yaya hafsat mai suna kausar tace yaya hafsat ni gaskiya tafiya zanyi kinga har 10:00pm ta buga ba zai yu na kwana anan saboda ban zo da kaya ba kuma gobe ina da "lecture" Hafsat ta ja d'an k'arami tsoki tace ko yanzu na kira wayar Abban fahad "still" wayar shi a kashe Raheela tabata fuska kamar za ta fashe da kuka, tace to yaya hafsat ki bari na hau "taxi" Hafsat ta zaro ido hade da cewa ba zan sake ki a dare nan ki hau "taxi" bara na kira Amar ya zo yadauke ki' Raheela tayi murmushin yak'e domin tasan mayuwaci abu ne yaa Amar ya zo yasauke ta Amar da na'eema na zaune a falon Amar yana duba wasu "file's" na'eema kuma na kallo "ringing" d'in wayar Amar ne yasa yadago daga abunda yakeyi, yadauki wayar gani suna yaya hafsat yana yawo a "screen" yasa yayi saurin "received" Muryar hafsat ce takarade masa kunne Amar don Allah ka zo ka dauki raheela' Yatsine fuska yayi daga bisani yace ni driver" ta ne da zan zo na d'auke ta ae ba da izzini na ta wanke kafa ta je gidanki' Yaya hafsat tayi murmushi tace don ni za ka zo ba don halinta ba "please Amar ka taimaka kayi min wannan "favour" Amar ya tabe baki yace naji gani nan zuwa batare da yajira jin ta bakin hafsat ba ya kashe waya, duk abunda yake fada bisa kunne na'eema saboda takasa ta tsare sai wani zarar idanu takeyi Amar ajiye "file" d'in ke rik'e da shi ya mik'e tsaye yanufi inda yake ajiye key's d'in mota yadauka na'eema ta mik'e a fusace tace yaa Amar wannan wane irin raini hankali ne"? Tsanani mamaki ne yarufe Amar kafin yabata, amsa tacigaba da fadar..... [23/07 4:29 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 6⃣8⃣ Wannan ae salon cin amana ne to wallahi" wallahi" matukar ka d'auki kafa ka je d'aukar raheela ni kuma sai na zantarda hukunci mafi muni akanka, domin nagaji da cin amana ta da ka keyi, har zobe ka je aka k'era maka mai Zane "heart" kasaka daya a hannu ka kasaka mata daya to kayi a banza saboda nariga na zana layi mai tsayi a tsakani Ku saidai S0 raheela ya zama ajalin ka amma bazaka taba samu ta a matsayin matar aure ka, ni d'inan da baka so nice abokiyar rayuwar ka ta har abada, shashasha kawai mai kwakwalwa tumakai Wanda baya gudun abin kunya mtss..taja tsoki ta haura "upstairs" da gudu tabar Amar tsaye kamar bishiya kwa-kwa ya sauke gwaro numfashi tsanani tsoron Allah ya kama shi, wai ni na'eema za ta wanke wa allo tabbas na'eema ta shuka mini rashin mutunci na nuna a gidan talabiji na BBC world" Ya kad'a kai yafice "driving" yakeyi amma ji yake kamar zuciyar'shi za tayi tsalle tafaso kirji shi tafito a haka yak'arasa gidan yaya hafsat, yana yi "parking" akafara yayafi dama garin yadau hadari a kasalance ya kira wayar yaya hafsat yace ki ce da ita tafito ya kashe, yaya hafsat tajuya wajen da raheela take zaune sai taga tadaura kanta a hannu kujera tana bacci, ta d'an bubuge ta, tashi tana bude idanu ta tace yaa Amar ya zo ne"? Yaya hafsat tadaga mata kai da sauri ta d'auki "handbag" d'inta tace sai da safe yaya hafsat tafita da gudu, tun daga nesa Amar ya hango ta ya girgiza kai ko yaushe raheela za ta girma tadaina gudu oho" Ta bude kofa tashiga tun kafi ta rufe kofa yafisgi mota da k'arfi gaske, raheela ta murguda baki suna fita unguwar su yaya hafsat aka sake da ruwa da k'arfi don haka Amar yak'ara "speed" dama gashi gwani ne a fagge gudu da mota, cikin 20 minutes" suka eso gida yayi "parking" daf da kofar shiga babban falon suka fito da gudu raheela tanufi kofa tana murda "handle" taji kofa gam Amar yakaraso yadaka mata tsawa yace kofar ma baza ki iya budewa sai na bude miki"? Har raheela ta bude baki ta bashi amsa yak'ara daka mata tsawa ta hanyar cewa, dallah bani wuri ta matsa masa yana Kama "handle" yana murdawa ya ji kofa a rufe ruff' Raheela ta kyakyale da dariya, wani mugun kallo ya watsa mata Wanda yayi sanadi da ta hadiye saura dariyar ta, yasoma "knocking" tun yanayi a sannu har yadawo yi da k'arfi daga karshe yadawo kwadawa na'eema kira, a hankali "window" ya bude na'eema ta lek'o kanta ta da sauri Amar yace na'eema wannan wane irin dabbanci ne da za ki rufe mana kofa kenan duk "knocking" d'in da nakeyi kina jina koh"? Saida tak'are musu wulaqantace kallo sannan tace, na rufe kofa kayi duk abunda za ka yi, gantalalu kawai, maciya amana sai kuma inda Ku ka saba zuwa kuna iskanci Ku, Ku kwana a chan. Wata irin zufa ce ta k'aryo wa Amar cikin sark'ewa halshe yace me ki ke nufi da na'eema"? Duk abunda na ke nufi kasani munafuki mai bak'ar fuska' Raheela kam mutuwar tsaye tayi yayida hawaye suka wanke mata, fuska cikin rawar murya tace haba yaya na'eema me mu kayi miki da ki ka zabi kiyi mana wannan mumuna k'azafi"? Na'eema tadaka mata tsawa ta kuma nuna ta da yatsa, tace ke k'arama karuwa rufe min baki ba da ke nake magana ba' Raheela ta kurma ihu tace yaya na'eema ni ki kira da karuwa kin manta ko ni wacece agareki"? Mtsss... Na'eema taja tsoki cikin zafin rai Amar yanufi window" yace ke na'eema yau na fahimce cewa wani Sabon hauka ki ke ji to zan sauke miki shi ki zo ki bude mini kofa' Na'eema ta kwabe fuska tace ba zan bude ba yau saidai ko kwana a waje amma ba dai a cikin gidanan ba 'yan iska kawai jarababu karaf ta rufe window" tayi tafiyarta. Raheela ta durkushe tana rusar Amar ya shure kofa da kafar shi, yasaki razanane ihu sakamako wani zafi da ya ziyarci kafar sa. Gani ruwa suna k'ara k'arfi yasa ya kalli raheela yace ke tashi mu tafi Tadago idanu ta da su ka kad'a sukayi jajir batare da tace komai ba tabi bayan shi ya bude mota yashiga ita ma tashiga a tunani ta fita zai yi sai taga yanufi "parking space" yayi parking yad'aura kanshi bisa "steering" raheela kuma tasaka kanta tsakiyar cinyoyi ta tacigaba da shashek'ar kuka.... Jeeddah Aliyu🌹 [23/07 8:33 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [23/07 6:46 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 6⃣9⃣ Tsawon lokacin suka d'auka a haka babu mai rarrashi wani, ga kuma ruwan da ake zangawa kamar da baki k'warya kamar daga sama raheela ta ji Amar ya bude kofa yafita tabishi da kallo, yanufi bakin "gate" d'akin Joseph yayi knocking" tana kallo Joseph yafito sukayi magana, yakoma d'akin shi, yayida Amar yajuyo bayan kamar dakika biyu zuwa uku sai ga joseph yak'ara fitowa hannu shi rik'e da "umbrella" yakare ruwa. Raheela tasauke numfashi, a zuciyata tace ko amfani me Joseph zai yi mana"? Amar yana k'arasowa yace ke fito' Cikin sanyi jiki raheela tafito, tabi bayan Amar ita dai fatan ta, taga wayewar gari lafiya tattara kayanta tabar musu gida tunda har na'eema tafara yi mata k'azafin zina kaitsaye "guest room" suka nufa Joseph ya bude kofa Amar ya masa godiya, yana shiga raheela ta rufa masa baya ta nemi daya daga cikin kujeri falon ta k'ame Amar yanufi "bedroom" yasaka key yabude kofa saidai kofar tak'i budewa, tsawon lokacin yad'auka yana fama da kofar ta bude amma tak'i cikin tsanani jin haushi da takaici yadawo ya zauna yadafe kanshi da ke barazana tsagewa gida biyu, a fakace raheela take galla masa harara saboda tafi jin haushi sa akan na'eema mtss...ta ja tsoki tafito da wayar ta, ta duba tym" rass gabanta yafadi sakamako gani 12:44am a zuciyata tace na shiga uku ba dai nufi yaa Amar anan za mu kwana ba, kai ina ba zata sabu ba bindiga a ruwa na kwana d'aki daya da yaa Amar kenan zargi yaya na'eema zai tabbata akan mu. Da sauri tadago tace yakamata ka koma wurin matarka kada zargin ta yak'ara tasiri akan mu, domin banga amfani zaman ka anan ba' A fusace yace in ki ka k'ara yi mini magana sai na fasa miki baki ko na tilassa ki kwana anan"? Kinga malama tun kafin nakasa "controlled" temper" na ki tashi kifita, jikinta na b'ari tanufi kofa saboda tayi masifa tsorata da shi ta bude kofa tafita, wata irin tsawa mai hade da walk'iya akayi raheela batasan lokacin da tattara siket d'inta ta kwasa da gudu ta koma inda tafito kallon d'aya Amar yayi mata kawarda fuska, ta lallaba ta nemi bayan kujeri ta rukube, a hankali tafara gyangyadi daga bisani ta kwanta k'asa bacci yayi awo gaba da ita, Amar ko ta kanta baiyi ba yacigaba da zance, zuci kamar ni na'eema zata wulaqanta"? tabbas na'eema tayi min abunda ba'a tab'ayi mini a tarihi rayuwa ta, wane irin jahilci ne ke damu na'eema da har yarufe mata ido take mana zargi zina"? Tsawon rayuwa ta bantaba kallon, wata 'ya mace naji ina sha'awa aikata zina da ita ballatana raheela da nakeso kamar numfashi na, ko a yanzu da na rasata rashi na har abada bantaba kallon ta, naji ina sha'awa aikata zina da ita, tabbas na'eema batayi mana adalci ba miyasa ta danganta mu da mumuna kalma mai matuk'ar zafi da dafi irin wannan"? Har k'arfe 3:35am Amar yana zaune ya buga d'an uban tagumi, sai faman tufk'a da warwara yakeyi daga bisani yadan kishigide da haka shima shugaba b'arayi na duk duniya ya sace shi. Kiran sallah da ke fita daga wayar Amar ne yayi sanadiyar falkawa Amar, a firgici ya tashi zaune yadafe k'ok'o kanshi nan take majigi kwakwalwa shi, yafara tariyo masa abunda yafaru da shi a watani baya, Amar ya kurma ihu hade da furta "oh no" Kamar a mafalki raheela taji ihun Amar a tsoroce ta, tashi zaune da rerafe ta k'araso gaban shi jikinta na rawa tace yaa Amar lafiya"? Wani mashahuri tsoro ne yak'ara lullube raheela Wanda yahaddasa mata zama babu shiri ba komai bane illah kukan da Amar yakeyi tamkar k'arami yaro, raheela tak'ara shiga rud'ani sakamako gani Amar ya durkushe k'asa yana kuka har da su shasheka abunda raheela a tarihi rayuwata bata tab'a gani ba babban mutum yana kuka ko babban shu'umi, hatsabibi, kuma miskili irin Amar tabbas k'azafi da na'eema tayi musu yataba shi. Gani yadda yake kuka yayi masifar bata tausayi karo na farko da raheela ta ji tausayi Amar ya ziyarce ta, ta matsa kusa da shi, tace don girman Allah yaa Amar kadaina kuka kowa yasan kai ba d'an iska bane, sharri ne kawai irin na yaya na'eema nasan dalilin da yasa tafadi haka saboda bataso zama na a gidanan, insha Allah gari yana k'arasa wayewa zan tattara kayana na bar mata gidanta domin banaso na zama silar rusa zaman auren Ku. Har raheela tadasa aya a zance ta Amar bai fasa kuka da yakeyi ba, ita ma batasan lokacin da tafashe da kuka ba sai ga Amar da raheela na kuka ba mai rarrashi wani..... [23/07 8:32 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 7⃣0⃣ Ba ka ji komai sai sautin kukan su da yakarade falon, raheela ta rik'o hannu Amar ta matsi cikin nata tace "for god sake" yaa Amar kayi hakuri kadaina kuka nan komai yayi zafi magani sa "Allah duk abunda mutum yayi don kanshi Amar yasauke ajiyar zuciya mai k'arfi gaske wata iska mai zafi tafito daga bakin shi tasauka a fuskar raheela ya zare hannu shi daga nata ya mik'e yafice, raheela ta bishi da kallon tausayi bayan fitar shi da kamar mintuna uku sai gashi yadawo ruwa da tagani a k'afafu shi yasa tagano alwala ya yi, tana kallon shi har ya kamalla sallah, da yake ita tana fashin sallah tsawon lokacin yad'auka yana addu'a hawaye na zuba daga fuskar sa, raheela tak'ara fad'awa a zango tunani to wai me ke faruwa da yaa Amar ne, kamar Wanda aka mintsina taga, mik'e yana huci yanufi kofa yanayi sa tamkar na mayunwaci zaki da yafito farauta, a firgici raheela tad'auki "handbag" d'inta tabi bayan shi hade da k'walla masa kira yaa Amar ina za ka tafi"? Ko juyowa baiyi ba ballatana tasa ran zai amsa mata gani yanufi cikin gida tasaki ajiyar zuciya, tafiya yakeyi amma ita da gudu take bin shi duk da haka takasa cinmasa hanyar "garden" yanufa ita dai raheela na biye da shi a maimako yashiga "garden" saida taga yabi wani d'an k'arami "corridor" wata kofa ta "glass" ya bude yashiga, a zuciyar raheela tace cab" dama da kofa a wurinan duk tsawon zama na a gidanan bansaniba"? Suna shiga ciki taci karo da tari "gym's machine's" a zube tace umh...ashe nan ne guy" nan yake barje gumi sa"? Suna wuce takarce k'arafai yak'ara bude wata kofa "exactly" irin ta farko raheela ta zaro ido sakamako gani wani had'ade falon kamar kana kasar nasara, kutt dama akwai irin wannan falon a gidanan bansaniba"? tana cikin kashe kwarkwata idanu ta, ta hango Amar yanufi wata kofa nan take tagano hanyar da za tabi tashiga d'akinta da sauri kuwa tanufi d'akin nata saboda gari ya waye tass" Amar yana bude kofa ya hango na'eema nade cikin "blanket" tana sharar baccinta cikin kwaciyar hankali yayi wani kukan kura chafko kafafu ta ya cillo ta k'asa kanta yadagi "bedside" tasaki razananiya k'ara yarufe ta da duka tamkar zai rabata da ranta cikin konar zuciya yace, kifad'a mini yadda ki kayi ki ka aure ni"? Duk tsanani zafin dukan da tasha bai hana mata tunawa da kashadi boka duguzuu kada Ku sake su kwana a d'aki d'aya duk ranarda suka kwana a d'aki d'aya asiri zai k'arye, na'eema tace wayyo Allah na asiri na yatonu dan Allah yaa Amar kayi hakuri wallahi ina sonka bazan iya rayuwa ba kai, tsanani takaici ne yarufe Amar baisan lokacin da yanushi bakinta jini yasoma zuba kamar anbude famfo kin cuce ni na'eema kinyi sanadi rabani da farin ciki na Allah ya esa tsakanina da ke da kyar na'eema ta mik'e ta arce na kare shima ya Mara mata baya tun kafin tak'arasa sauka daga "upstairs" ya cima tun daga sama yake yana jingar ta har suka sauko k'asa raheela da ke had'a kayanta taji ihun na'eema yacika gida da gudu tafito, ta hango Amar yana ta faman "ball" da na'eema gaba d'aya fuskarta tarine da jini a gigice ta esa wurin Amar ta chakume shi, tace kan'ka d'aya kuwa yaa Amar kashe ta za kayi"? A harzuk'e yace ko na kashe ta bazan huce takaici da bakin ciki abunda ta haddasa min, raheela wannan da ki ke gani muguwa ce azzaluma ce batada imani ta rabani da ke bayan tasan ke ce farin ciki na shikenan na'eema kin wargaza min rayuwa kin rusa duk wani gini na rayuwa ta, domin raheela ita ce rayuwa ta yana karasa zance sa ya zube k'asa yafashe da matsananci kuka raheela tafara ja da baya tsawon rayuwa ta batada amincewa da Amar yana sonta sai yau saida takai karshen bango ta sulele k'asa ta zauna tajuya ta kalli Amar yana durkushe yana kuka ta juya wajen na'eema tana kwance a k'asa ta rusar kuka baki da hancinta na zubarda jini, raheela tafashe da kuka tace me ke shirin faruwa da mu"? Wane irin sabon al'amari ne yake yunk'uri kunno kai a zuri'ar mu"? Amar yad'ago jajaye idanu shi yanuna na'eema da yatsa yace na rantsi yadda narasa raheela ke ma kin rasa ni har abada saboda bantaba jin na tsani wani mahaluki irin yadda na tsane ki banaso na cigaba da bude idanu na ina gani ki a matsayin mata ta don haka tashi, mu tafi Kaduna a gaban iyayye mu kifad'a musu yadda akayi ki, ka aure ni daga nan ni kuma zan tsintsinka duk wata igiya da ke tsakani mu na'eema na ji abunda Amar yafada tak'ara rushewa da kuka nan take tafara nadama abinda ta aikata, cikin zafin nama yafisgo ta yanufi waje da ita da sauri raheela tashiga d'aki ta kinkimo "trolley" ta da kyar take jan ta Amar ya wulga na'eema cikin mota Joseph yak'arasa wurin raheela ya karbi trolley" d'in yasaka mata a mota, gani na'eema da trolley ta a baya yasa dole ta zauna "seat" d'in gaba Amar yafisgi mota da k'arfi Joseph yabude gate kamar walkiya haka yafice daga unguwar........ Jeeddah Aliyu🌹 [25/07 8:51 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [24/07 7:25 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 7⃣1⃣ Gudu yakeyi kamar zai tashi sama mota har wani tsalle takeyi, na'eema na ta faman rusar kuka, raheela tajuya wurinta tace yaya na'eema zuwa wannan lokacin yaci ace kidaina kuka domin duk abunda ake gudun afkuwa sa yafaru, kamar raheela na k'ara zugata tak'ara rushewa da wani sabon kuka' Tsanani gudun da Amar yake shararawa yasa cikin d'an k'ank'ani lokaci suka shiga garin Kaduna, na'eema nagani sun eso gida tak'ara fashewa da kuka shikenan yau ce ranar tono asiri mu miyasa nayi sake har shedan ya rinjeyeni na aikata abunda, zai dameni"? Kaicho na wallahi nayi nadama bin tafarki umma domin gashi nan yakaini yabaro ko da wane idanu zan kalli Daddy da Abba"? Amar yanayi "parking" yafice daga motar yanufi "part" d'in kaka, raheela tafito gani na'eema batada niyar fitowa yasa ta rik'o hannuta kaitsaye su kanufi inda Amar yadosa. Kaka na zaune a falonta, hannuta rik'e da rediyo tana sauraro taji anbude kofa tana dagowa tayi ido biyu da Amar tace lalle marhaba da likita bokan turai zuwa bazata akayi mana irin wannan samak'o har ina"? Amar dai bai ce da ita komai ba yanemi kujera ya zauna, raheela da na'eema suka shigo kamar makafi raheela na gaba rik'e da hannu na'eema kaka tajuyo tana k'are masu kallo yanayi su tamkar na makaho da d'an jagora mamaki ne yakusa somarda kaka sakamako gani na'eema jina-jina daga ita sai rigar bacci kanta ba d'an kwali gashinta kanta a ya motse k'afarta ba takalmi gaba d'aya ta fita haiyaci ta, kaka ta mayarda ganinta wurin raheela tana sanye da riga da siket na atamfa saidai babu mayafi a jikinta, idanu ta sun yi jajir gani su a haka yasa kaka tagano akwai matsala babban ta girgiza kai hade da tabe baki, raheela da na'eema suka nemi matsugunni suka zauna, na'eema tacigaba da kuka yayida raheela ta zanga tagumi falon yakarad'e da sautin kukan na'eema da rediyo kaka daga bisani kaka ta kashe rediyo ta, sai sautin kukan na na'eema yak'ara armashi kaka ta d'auki tsawon daki'ka biyar tana kallon su daga bisani tasauke gwaron numfashi, tace kai saurareni karku mayarda ni sakarai mana ya za'ayi Ku shigo min falon cikin bakon yanayi sannan kowane Ku yayi shiru kuna nufi baza Ku sanarda ni abinda yake faruwa ba"? Amar yayi huci kamar bak'in kumurci cikin tafarfasa zuciya, yace kaka na'eema ta cuci ni ta haddasa mini cutar da ba zata taba warkewa wallahi na tsaneta kaka na tsani na'eema bana sonta domin tayi sanadi nisanta ni da mafalki na tarabani da mahadin rayuwa ta kaka miyasa na'eema ta aure ni bayan tasan ba ita ce zabi na ba"? Shikenan kaka yanzu narasa raheela kinfad'a min yadda zan yi raheela tadawo gareni domin rashinta a gareni tamkar narasa numfashi na ne. Kaka ta numfasa tayi murmushi hade da cewa babbar magana, lalle wannan shi ake kira da ana wata ga wata Ka tashi sawu ka a likkafa kad'auki matar ka Ku je chan wurin iyayye Ku su nema muku mafita, lokacin da nace ban amince da aure Ku miyasa iyayye Ku basu tambaye ni da dalili ba, sai ya zo da ta kwabe muku za Ku zo min to ni babu ruwa na a cikin wannan al'amari naku' Ni fa bana cikin haiyaci na koda na aure ta yanzu kuma ina cikin natsuwa ta bazan iya cigaba da zama da ita ashirye nake na fuskaci kowane irin k'alubali da zan gujewa auren wannan munafuka, yana k'arasa zance sa yafice daga falon a fusace kaka tace dawo ka kwashe min ita anan Amar yayi banza da ita kaka tajuya wurin na'eema ta kyabe baki tace dadi na da gobe sauri zuwa, dama abunda ka shuka shi za ka girba kin cuci kanki na'eema kinyi fatali da kyakyawar tarbiyarki kinbi mumuna tafarki uwarki gashinan takai ki tabaro, ta jefa ki cikin masifa da bala'e ta had'a da hudubar shedan gashi tun tafiya batayi nisa ba kinfara fuskanta tasko da wulaqanci d'a namiji wannan k'adan daga cikin masifar da za ku fara fuskanta kenan matukar baki tuba ba ki kadaina bin bokaye da 'yan tsinbo wallahi karshen ki bazaiyi kyau ba. Na'eema tafashe da kuka mai matukar ban tausayi, ta zube gaban kaka tace wallahi na tuba kaka nayi nadama sharrin shedan da son yaa Amar ne yajanyo mini na jefa kaina cikin wannan masifa ki yafe min kaka ki rok'a mini gafara yaa Amar da raheela domin na cutarda su tak'arasa magana hade da rusa ihun kuka' Tausayi ta yakama kaka domin tasan na'eema natsatsiya yarinya ce duk wannan abun da ta aikata hudubar uwar ta ce da kuma son da take yiwa Amar, cikin tausayawa kaka tajanyo ta jikinta tasoma rarrashinta tace tadaina kuka na'eema kowane dan-adam aziji ne baya wuce kuskure tunda har kinyi nadama abunda ki ka aikata sai ki nemi gafarar ubangiji domin shi, gafuru rahim ne' Na'eema tace na gode kaka tajuya wurin, raheela tace lil sis ki yafe min nasan na cutarda da ke nayi yunkuri jefa rayuwarki cikin masifa da bala'e amma daga karshe jefa da nayi yadawo kaina, [25/07 2:52 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 7⃣2⃣ Da sauri raheela ta rufe mata baki tace na yafe miki yaya na'eema, kuma inaso kisani bantab'a son yaa Amar ba kuma har abada zuciyata ba za taba son shi " I promise you yaya na'eema no matter what's happen" yaa Amar ba zai taba samu gurbi a zuciyata na'eema ta rungume raheela tace na gode lil sis ba zan taba manta d'inbi alkhairi ki agareni raheela tayi murmushi jin dadi tsanani farin ciki ya baiyana akan fuskata mafalki ta ya tabbata yau ta shirya da yaya na'eema. Kaka ce ta kaitsi musu hamzari ta hanyar fadar Ku tashi mu tafi b'angare iyayye Ku ayita ta k'are nan take jikin na'eema yafara b'ari idanu ta suka ciko da kwalla kaka ta kalle ta, ta kyabe baki tace dole kitashi don ni banida magani da zanyi miki, tsuntsu da ya kira ruwa shi ruwa kan d'oka ae dama duk mutumi da yabiye son zuciya to fa dole juri gwagwarmaya tashi maza mu tafi tun kafin na cire hannu na daga sha'ani Ku' Raheela ta rik'o hannu na'eema had'e da cewa tashi mu tafi yaya na'eema, insha Allahu ba abunda zai faru sai al-khairi cikin mutuwar jiki na'eema ta mik'e kaka ta jefa mata hijab tace ae sai ki suturta jikin ki koh"? Raheela tasaka mata hijab d'in tana k'ank'ame da hannu raheela suka nufi "part'' d'in su Amar. Kaka na gaba suna biye da ita kaitsaye falon Alhaji Muhammad matawalle duka dosa, kaka ce tayi sallama, daddy na kishigide hannu shi na rik'e da "newspaper" mami na zaune kusa da shi tana had'a masa "tea" a lokacin d'aya daddy da mami suka amsawa kaka sallama, gani raheela da na'eema a bayanta yasa daddy ya mik'e zaune da sauri domin yasan ba lafiya musanman da ya hango fuskar na'eema a kunbure, mami tasaki baki da hanci tana kallon abin mamaki' Kaka ta nemi kujera ta kame, raheela da na'eema suka yada zango a k'asa kowace su ta sunkuyarda kai a kas' yanayi su tamkar na masu d'aukar karatu, daddy yace me ke faruwa hajja ina ki ka had'u da wadanan"? Yakarasa magana had'e da nuna su da yatsa, kaka ta tabe baki ta kuma gyatsine fuska daga bisani tace Amar ne yakawo su yadawo muku da 'yar Ku na'eema domin baisan ya akayi ya aure ta ba a tak'aice Amar dai yace ba na'eema yake so ba sai kusan yanda za kuyi da 'ya'ya Ku' har kaka ta dasa aya a zance ta daddy da mami na kallon ta mami ce tasami k'arfi guiwa yin kalma shahada tanayi tana tafa hannaye, tace na shiga uku ni fateema wace irin masifa ce Amar yake kokari kuno kai da ita"? Daddy yayi gyaran murya, had'e da kad'a kai yace ina shi Amar d'in yake"? Kaka tace oho! Daddy yak'ara harzuk'a yace wannan ae wulaqanci ne ya za'ayi ya zo da babbar magana irin wannan kuma yasaka k'afa takalmi yayi tafiyar sa haka daddy yadinga zanga fada kamar zai ari bakin kare, daga bisani yajuya wurin mami yace ke d'auko min waya ta har ni Amar zai kawowa iskanci wallahi yau zai had'u da bacin rai na so ke ya tarwatsa mana zumunci ni da d'an uwana, mami ta mik'a masa waya cikin konar zuciya yadanno number" Amar, ga mamaki sa sai yaji "ringing tone" d'in wayar Amar a cikin falon" daddy yana dagowa ya hango Amar tsaye a bakin kofa, harara daddy ya galla masa yace to isashe ae sai ka shigo da kayiwa mutane tsaye a bakin kofa Amar yak'araso yanemi kujera ya zauna, daddy sake danna number" Abba ta bangare Abba kuwa yana zaune a falon umma hajara na gefen shi, aunty Amarya kuma tashigo falon hannuta d'auke da katon "tray" dai-dai lokacin wayar Abba tayi "ringing" gani suna d'an uwanshi yasa yadaga da sauri daddy naji Abba yadaga kiran yace Abdullah ka tattaro iyalinka duka ka zo da su "part" d'ina akwai magana daddy na k'arasa fadar haka ya kashe waya, cikin hamzari Abba ya mik'e had'e da cewa ku d'auko mayafai ku mu tafi "part" d'in yaya karaf umma hajara tace yau kuma "assembly" safe aka tsiro mana"? To Allah yasa mu ji alheri, Abba ya girgiza kai yasa kai yafita' Suna shiga falon kowane su yayi turus musanman umma hajara da ta hango na'eema a tak'ure tana rusar kuka daddy yace bissmillah Ku zauna mana..... Jeeddah Aliyu [25/07 8:51 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [25/07 7:41 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 7⃣3⃣ Daddy ya kwashe bayani da kaka tayi masa ya fada musu, tun kafin daddy ya dasa aya umma hajara ta zabura cikin hargowa tace, wannan ae wulak'anci ne duk tsawon zaman da yayi da na'eema bai bullo da wannan makirci ba sai zuwa bak'ar annoba nan gidansa in har ka gaji da 'yata ka sake ta mana ke hajara banaso shirme Abba ne ya takawa umma hajara birki in ki ka kuskura na k'ara jin kin furta uffan a zance nan wallahi sai nayi mumuna saba miki' Dole umma hajara ta kame bakinta sai wani muzurai takeyi, daddy ya juya wurin Amar yace Amar me ka ke nufi da ba'a haiyaci ka ka aure na'eema"? Iya sanina da amincewa ka mu ka aure ma na'eema duk ciki Ku ba Wanda aka yiwa dole ka, gaugauta sanarda mu manufarka domin nasan irin kala hukunci da zan yanke akanka' Amar yad'ago jajaye idanu sa yace wallahi daddy bantaba son na'eema ba, ban kuma taba kallon ta a matsayin wance zanyi rayuwa aure da ita saboda zuciyata raheela take so kaka sheda ce akan irin son da nake ma raheela wani abin mamaki sai gashi na waye gari da aure na'eema daddy bana sonta, wallahi bana sonta ku taimake ni ku ceto rayuwa ta daga halaka ku rabani da na'eema domin ba ita bace zabi na cigaba da zama da ita zai iya haddasa mini shiga k'unci da matsala fiye da wanda nake ciki a yanzu. Har Amar ya dasa aya ba wanda yayi yunk'uri katsi shi, daddy yak'ara juyawa wurin na'eema yace daina kuka na'eema ki fada mana iya gaskiya abinda ki ka sani cikin wannan sark'ak'iya"? Cikin muryar kuka na'eema ta fayyace irin ta'asa da suka aikata ita da umma hajara, gaba d'aya falon suka d'auki kalma shahada bayan falon yayi tsit kaka gyara zama tace ni kai na naciro laya cikin pillow raheela shiyasa lokacin da Amar ya zo da zance aure na'eema nace ban amince ba domin nasan Amar raheela yake so" Abba ya mik'e cikin tsanani bacin rai ya shararawa umma hajara tagwaye mari, yace tir da halinki hajara nayi danasani kasance wa miji agare ki, zama da mace mai irin halaye ki masifa ne kin cuce ni kin gurbatawa 'yata rayuwa, kuma wallahi indan wani abu yasami raheela sai nayi shari'a da ke ba zan iya cigaba da zama da ke don haka ki je na sake ki, Saki d'aya, sakamako jin furucin abba na karshe ya haddasawa umma hajara kurma ihu ta zube gaban tana kururuwa had'e da bashi hankuri ka dubi girma Allah" abdullah kayi hankuri kayafe mini wallahi sharri shedan ne, a wannan shekaru ka sakeni ina ka keso na dosa ka rufa mini asiri kadawo da ni d'akina' Abba galla mata harara yace wane d'aki ae ke yanzu bakida d'aki a gidanan. Umma hajara tasake rushewa da kuka tarerafa gaban kaka tace na tuba hajja ki sa baki yadawo da ni d'akina, kaka tasauke gwaro numfashi tace tashi ki zauna, ae kuwa da sauri umma hajara ta kai zaune' Kaka tayi gyaran murya tace kayi hankuri Abdullah tabbas hajara ta aikata mumuna aiki amma tunda tagano kuskure ta sai kayi mata afuwa kadawo da ita ko don albarkaci 'ya da ke tsakani ku da kuma matsayin ubanta a gare ka, kai kuma Amar ba abinda za muyi maka illah mu baka hankuri ka daure ka rarrashi zuciyar ka, ka cigaba da zama da na'eema, saboda raheela ta haramta agareka Allah, ya k'addari na'eema ce matarka. Amar yayi shiru hawaye na zuba daga idanu sa, daddy yace abinda hajja tafad'a gaskiya ne Amar ka rungume k'addara zama da na'eema, a matsayi na na mahaifika na umarce ka da ka zauna lafiya da matarka ka bata hak'oki ta da suka rataya a wuyanka kuma daga yau na soke zance raheela, ka manta da kataba son wata raheela, kafara shirya sabuwa rayuwa da na'eema da sannu za ka ji kafara sonta. Abba yace karka tilassa masa zama da ita domin baya sonta, ka barshi yaji da zafi d'aya na rashin raheela "daddy yad'agawa Abba hannu yace karka dawo da hannu agogo baya Abdullah na riga na yanke hukunci kuma bana tunani zan chanza ra'ayi na akan hakan, gaba d'aya falon aka cigaba da rarrashin Amar, shi dai binsu da ido yakeyi saboda ya fahimci basusan zafin son ba daddy yacigaba da cewa na baka awa d'aya ka tattara matarka Ku koma abuja kai, kuma Abdullah kadawo da hajara shikenan na rufe wannan maganar banaso ak'ara tadata. Abba yace ba'aso raina hajara zan dawo da ke sai don albarkaci magabata na don haka nadawo da ke ina rok'o ki, da ki cigaba da halinki karki fasa Abba yana k'arasa fadar haka ya mik'e yafice daga falon kaka tariko hannu raheela suka marawa Abba baya daga nan kowa Yakama gabansa falon yarage daga daddy sai Amar, daddy yadafe kafad'ar Amar yace kayi hankuri Amar nasan za kayi tunani nayi maka rashin adalci ta hanyar tilassa ka zama da na'eema, ni kuma zumunci mu ne banaso yasami matsala, ka zauna da matarka lafiya Allah yayi maka albarka tashi katafi cikin mutuwar jiki Amar ya mik'e zuciyarsa tamkar garwashi yafice daga falon yanufi "part" d'in kaka...... [25/07 8:50 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 7⃣4⃣ Yana shiga falon kaka ya zube a gaban kaka yafashe da kuka kamar k'arami yaro, cikin shasheka kuka yace banaso na'eema kaka bazan iya zama da ita duk lokacin da na kalle ta sai naji na tsane ta kaka ta girgiza kai tausayi Amar yakamata, tace bakada mafita Amar da yawuce cigaba da zama da ita kayi biyayya da umurni mahaifika da sannu za ka ga amfani hakan kaka tacigaba da yi masa nasiha had'e da kalamai masu dadi. Duk abunda ke wakana tsakani kaka da Amar raheela na cikin "bedroom" tana jin su tace Allah sarki hero ashe da gaske ne kana sona, saidai kash ka taki rashin Sa'a domin ni bana sonka. Ta bangare umma hajara kuma tana shiga bedroom d'inta na'eema na shigowa, ta rungume umma hajara tace kiyafe mini umma nasan za ki ji ciwo na fallasa asiri ki a baina jama'a banida yadda zanyi ne, umma dole na fad'a domin mu zallunci Amar da raheela, ni kan nayi nadama umma ke ma ina rok'o ki da ki zubarda duk wata kiyayya da ki ke yiwa raheela, cikin zafin zuciya umma hajara ta ture na'eema ta nuna ta da yatsa tace kiyayya yanzu nafara nunawa raheela ita tunda har tayi sanadi da igiya aure na d'aya ta tsinke ni kuma nasha alwashi sai naga bayanta, yadda nakeji kiyayya raheela a raina Sam banaji ta uwata Sadeeya don haka yaki yanzu aka fara tabbas sai naga bayan raheela maza ki tashi ki fita min daga d'aki banaso ganinki duk yadda na'eema taso ta bawa umma hajara hankuri tayi amma daga karshe kora kare tayi mata ta rufe kofarta, na'eema na kuka tanufi "part" d'in kaka tsawon lokacin kaka tad'auka tana musu nasiha na'eema ta mik'e tanufi bedroom wurin raheela tak'ara bata hankuri raheela ta share hawaye ta, tace komai yawuce yaya na'eema ki shiga "bathroom" kiyi wanka bayan na'eema tafito daga wanka, raheela tabata kaya tasaka, muryar daddy suka ji yana cewa ke na'eema kifito ku tafi, na'eema tace lil sis d'auko kayanki mu tafi, raheela tayi murmushi tace bangaji da gani kaka ba sai gobe zan dawo, duk yadda na'eema taso raheela ta bisu amma raheela tak'i na'eema tajuya tafice idanu cike da kwalla Amar yana ganinta yafice daga falon, har wajen mota kaka da daddy suka raka su, raheela ta labe a jikin kofa tana kallon su karaf suka had'a ido da Amar gabanta yayi masifar fad'uwa wani irin sanyi yasoma ratsa k'assa ta da sauri ta d'auke idanu ta, tana kallo har yaja mota yafice daga gidan da kyar raheela ta ja k'afafu ta tashiga bedroom" tayi kwance nan take zazzabi mai zafi yarufe ta. Tun lokacin da suka d'auki hanya Amar ya kunna "tape" kaset d'in kira'a sheikh husary cikin suratul al-araf yana bi kira'ar a hankali nan take yaji wata natsu tashige shi, saidai yadda yake tsulla gudu abun babu kyau kamar daga sama ya hango garke shanu taf da titi yayi k'okari ya kauce musu inda yadosa baisan akwai wata mota tafe cikin gudun bala'e fiye da gudun da yakeyi nan take motocin sukayi k'azamar haduwa, hatta da engine motar Amar saida ya watsi daga mutane suka kawo musu agaji da kyar aka Ciro Amar da na'eema kowane su kamanu da halitta sa tasauya babu alamu numfashi a tare da su hukumar kare hadari da ababe hawa wato "road safety" su suka d'auki gawarwa ki su Amar zuwa asibiti da yake basu fita daga garin Kaduna ba hadari yafaru. Daddy da Abba suna zaune a falon kaka aka kira wayar daddy yana dagawa yasake salati had'e da jefarda waya..... Jeeddah Aliyu [27/07 7:32 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [27/07 5:23 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 7⃣5⃣ Abba yarik'o hannu daddy yace me ke faruwa ne yaya"? Cikin sak'ewar halshe daddy yace Amar da Na'eema sunyi "accident {hatsari} a lokacin d'aya Abba da kaka suka d'auki kalma shahada, Raheela da ke kwance a d'aki tana jin abinda daddy yafad'a taji, mumuna fad'uwar gaba da sauri tadafe k'irjinta, tace "innalillahi wa'inna illahi raji'um" da kyar ta mik'e tanufi falon tana shiga daddy da Abba na ficewa da sauri tafad'a jikin kaka tafashe da kuka, kaka tace ba kuka za kiyi ba maza d'auko hijab d'inki mu tafi asibiti d'in Raheela ta koma d'aki sai gata tafito sanya da hijab suka fice ita da kaka kaitsaye "part" d'in Mami suka shiga mami na zaune a falon da alamu su daddy basu sanarda ita abunda ke faruwa ba, gani Raheela tashigo da kuka yasa mami tace lafiya me ki ke yiwa kuka"? Kaka ce tayi k'arfin hali sanarda mami nan take jikin mami yafara rawa, ta mik'e tashiga d'aki tasako hijab tace hajja mu tafi kaka tasauke numfashi had'e da cewa Sadeeya da hajara basuda lafiya abinda yake faruwa ba ki shiga ke da Raheela ki sanarda su ni ina wurin mota kuma dan Allah karku bata lokaci, hankali na a tashi yake' Mami na gaba Raheela na biye da ita a babban falon suka tararda aunty amarya, mami tayi mata bayani a gaugauce daga bisani tashiga d'aki umma hajara tana kwance bisa gado sai sak'e-sak'e yadda za ta ga bayan Raheela takeyi, mami tayi sallama a wulak'ance umma hajara ta amsa tayi wani kwabe fuska kamar kashi shanu, tace me kuma aka zo nema a wurina"? Tsofafi munafukai duk munafuci Ku akanku zai k'are ni naci dubu sai ceto duk uban da yaci tuwo da ni mi.....dallah dakata hajara ni ba wannan ne yakawo ni d'akinki nq zo ne na sanarda ke 'yar da ki ke haukata akanta to sunyi "accident"{hatsari} kuma ba wanda yasan halin da suke ciki suna raye ko suna mace Allah ne masani don haka in kinga dama ki d'auko mayafi ki mu tafi asibiti, umma hajara ta d'ora hannu aka ta rusa ihu had'e da k'unduma asshar mami ta zaro ido tace wa'iyazubillah" hajara kina da hankali kuwa"? Na rantsi da Allah indan wani abu yasami 'yata wallahi sai na d'auki mumuna famsa akan Amar da Raheela Hmm...cabdijam lalle hajara bakida imani jahilci ki babba ne ni kan kinga tafiya ta, umma hajara tacigaba da gunji kuka da sambatu marasa kan gado, a "parking space" mami ta tararda kaka, aunty amarya da kuma Raheela da ke ta sharb'a kuka cikin sanyi jiki mami tace mu tafi batare da kowa ya tambaye ta umma hajara ba suka Shiga mota "driver" yaja mota mami ta kira daddy yafad'a musu sunan "hospital"{asibiti} d'in da suke saidai har yanzu babu wani kwa-kwara bayani akan su, mami ta kashe waya had'e da share hawaye da suka zubo mata, umma hajara na fitowa tafara kwad'awa d'a audu kira da gudu yak'araso wurin ta tace mu tafi ka kaini asibiti ka bi bayan munafukai chan, a lokacin d'aya sukayi "parking" a "reception" suka tararda su daddy zaune sai kuma nazee da ya zo daga baya, cikin ihu da kururuwa umma hajara tashigo "reception" d'in tamkar mahaukaciya wayyo na shiga uku na lalace shikenan sun kashe mini ita, me nayi muku mutane da Ku ka zab'i hanyar rabani da 'yata ita kenan gareni' Ke"hajara wannan wane irin sakarci da rashin yarda da k'addara ne"? Abba ne yadaka mata tsawa, kin isa ki hana ubangiji yi iko sa ne"? Nan take umma hajara ta natsu amma duk da haka bata fasa gunji kuka ba tanayi tana fayyace majina da gefen hijabi ta. Tsawon awa d'aya sukayi a zaune daga bisani suka sami gani likita da ya jagoranci duba Amar da na'eema daddy da Abba na zaune a "office" d'in doctor Abbas A Abbas ya cire farin gilashi sa yak'are wa su Abba kallo yasauke gwaron numfashi, daga bisani yace Alhaji saidai kuyi hank'uri da sauri daddy da Abba suka fara furta kalma "innalillahi wa'inna illahi raji'um" Daddy yace sun mutu koh likita"? Abba yace mu musulmai ne mu yarda da k'addara dama duk mai rai mamaci ne Allah ya jik'ansu ya gafarta musu' Dr Abbas yayi murmushi yace Alhaji ba Ku jira na k'arasa zance na kun yanke hukunci, daddy yace Dr ba wani zance da za ka k'arasa a gaban mu aka fita da gawar aboki hatsari su. Dr Abbas ya Shafa sak'o sa yace Alhaji 'ya'ya Ku suna raye basu mutu ba, saidai suna ciki "critical conditions" mu samu mace tafarfad'o amma Dr Amar zuciyarsa kadai ke aiki kuma yasamu "injury's" da yawa daga ciki harda kariya a k'afarsa ta hagu da hannu sa na dama ita kuma mace tasami kariya a cinya da kuma hannuta, ga kuma "internal injury's" saboda kanta ya bugu duk da haka ita tafarfad'o mu yi mata allura bacci ne za ta farfad'o "around" 6:00pm insha Allah in tafarfad'o za Ku iya ganinta amma Dr Amar sai yadda hali yayi... [27/07 7:31 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 7⃣6⃣ Daddy da Abba suka share gumi ciki yanayi na mutuwar jiki suka fito "office" d'in Dr Abbas da sauri mami da kaka suka had'a baki wurin tambaya Alhaji ya jikin su"? Daddy yasauke ajiyar zuciya yace na'eema tafarfad'o sunyi mata allura bacci sai k'arfe 6:00pm zata farfad'o amma Amar ba wani kwakwara bayani akan shi, umma hajara tasaki ajiyar zuciya mai k'arfi gaske duk Wanda ke wurin saida yajuyo ya kalle ta tace Alhamdulilah"! Kaka, mami da kuma aunty amarya suka fashe da kuka, Raheela ta zube kasa da sauri Nazee ya taro ta, Raheela tafashe da kuka gwanin ban tausayi daddy da Abba suka nufi massllaci da ke cikin asibiti domin sallah azhar, Nazee ya kalle kaka yace kaka jikin raheela yayi zafi sosai da alamu zazzabi mai zafi ne yakeso yarufe ta, kafin kaka tabashi amsa umma hajara, tayi karaf tace yoo" ae dole tayi zazzabi tun da abokin shashaci ta rai a hannu Allah" A harzuk'e kaka ta mik'e ta wankawa umma hajara mari hawaye na zuba daga idanu kaka, tace tir da halinki hajara ke kan kin zama annoba haihuwa ki batayi yiwa iyayye ki rana sun haifo masifa da bala'e rashin imani ki a baiyane yake ae ko ba komai Amar mijin 'yarki ne ki tuna da irin zalunci da Ku kayi masa, duk da haka Amar yayi biyayya da umurni mahaifi sa ya amince zai zauna da 'yarki shine yanzu ki ke binsa da mugaye kalamai to ta Allah ba taki ba insha Allah Amar zai mik'e da k'afafu sa, in yaso sai ki had'iye zuciya ki mutu don bak'i ciki umma hajara ta sunkuyarda kanta kasa tana huci aunty amarya, ta mik'e ta rik'o hannu kaka tace yi hak'uri hajja karki biye mata Ku saida hali domin ita abin kunya gaba taba shi ba baya ba, ba Amar take k'i ba Raheela ce bataso wallahi na tabbata da hajara na da yadda zatayi da yanzu tayi domin ta kawarda Raheela a doro k'asa kwana ta ne kawai ke gaba' Kaka ta koma wurin zamanta ta zauna, Raheela tak'ara fashewa da kuka mai cin rai cikin bacin rai Nazee yaja hannuta suka fita. *6:00pm* Kamar yadda Dr Abbas yad'afa 6:00pm na bugawa na'eema tafarfad'o, gaba d'aya su daddy suka zagaye ta sunayi mata sannu saboda zafin ciwo da kyar take amsawa ta juya wurin daddy muryar ta na fita a hankali tace daddy ina yaa Amar"? Daddy yakasa bata amsa saida Abba ya ari bakin sa yaci masa albasa yace Amar na nan na'eema jikinsa da sauki, tayi shiru tana kallon mutane d'akin daga bisani tace Abba ina umma taa da Raheela"? Da sauri umma hajara tace gani nan na'eema tak'araso kusa da ita na'eema tacigaba da cewa Dan Allah umma kiyi hak'uri kiyafe min umma hajara ta share hawaye tace na yafe miki na'eema Allah yatashi kafad'a ki' "Ameen" umma tajuya wurin da Raheela take tsaye ta jingina jikinta da bango tace zo nan Lil sis" Raheela tak'arasa wurinta na'eema ta rik'o hannuta tace Raheela kiyafe mini abinda nayi miki ki kuma rok'a mini yaa Amar ya yafe mini nasan na cutarda Ku amma a yanzu nayi nadama, kiyi mini alk'awali ko bayan raina za ki kulla min da umma taa saboda umma batada kowa sai niya, banaso tayi kukan rashi ni ki maye mata gurbi na raheela tafashe da matsanaci kuka tace nayi miki al'kawali yaya na'eema zan kula da umma tamkar yadda zan kula da mahaifiya ta. Na'eema ta k'ara juyawa wurin umma hajara tace umma ga raheela nan kiyi mini alk'awali za ki d'auke ta tamkar yani umma Raheela na sona tana son farin ciki na Dan Allah umma ki so ta kidaina nuna mata k'iyayya kinji umma naa"? Na ji na'eema nayi miki alk'awali zan so Raheela tamkar 'yar da na Haifa Allah yabaki lafiya" Na'eema tajuya wurin su mami tace kaka, mami aunty amarya Ku yafe mini gaba d'aya suka fashe da kuka kowane yana fad'ar na yafe miki Allah ya baki lafiya" Dr Abbas ne yashigo yace wannan wane irin abu ne za ku saka maras lafiya a gaba kuna kuka"? Dan Allah Ku fita a lokacin d'aya su mami suka fice yayi saura daga daddy sai Abba suka rage har sun juya na'eema ta kira su tace daddy da Abba dan girman Allah kuyi mini alk'awali bayan raina za Ku aurawa yaa Amar, raheela saboda ita ce farin ciki sa. Daddy da Abba suka goge gumi had'e da kallon junan su na'eema ta katsi masu hamzari ta hanyar cigaba da rok'o su daddy yace mu yi miki alk'awali na'eema kuma insha Allahu za mu kasance musu cika miki alk'awali daga nan Dr Abbas ya gargad'a su daddy waje na'eema ta bi su da kallo idanu ta na zubarda hawaye. Tun da misali k'arfe 11:00pm jikin na'eema yayi tsanani sai Amai jini takeyi kusan likitoci hud'u ne akanta da misali k'arfe *5:00am* na asuba na'eema tace ga garin Ku rai yayi halinsa rai bak'o duniya *innalillahi wa'inna illahi raji'um* *k'ulli nafsi za'ikatil mauti* *Duk mai rai mamaci ne Na'eema ta tafi tabar duniya ko me zai faru in umma hajara taji mutuwar Na'eema*? Jeeddah Aliyu🌹 [30/07 8:50 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [29/07 1:06 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 7⃣7⃣ Dr Abbas yafito daga d'akin da na'eema take, yana share gumi da farin _handkerchief_ da sauri daddy yanufi wurin shi Dr ya jikin nata"? Dr Abbas yayi shiru daga bisani yace _I'm sorry 2 said_ na'eema ta rigamu gidan gaskiya _innalillahi wa'inna illahi raji'um_ kalma da daddy yake ta mai-maitawa Abba yak'araso wurin daddy yadafa kafad'ar sa yace Allah da yabamu na'eema shi ya k'arbi abar sa kuma yafi mu sonta a yanzu tsakani mu da ita sai addu'a _Allah ya jik'anta ya gafarta mata zunubai ta Allah ya kyautata makwacinta_ daddy yasauke numfashi yace *Ameen*. Daddy da Abba suka nufi _reception_ inda kaka da umma hajara suke dama su kadai suka kwana a _hospital_ d'in cikin sanyi murya Abba yace hajja Allah ya k'arbi ran na'eema, yanzu nan za'a fito da gawar ta. Kaka tasaki kalma shahada yayida umma hajara ta kwatsama ihu, tafara zanga sambatu _wayyo ni Allah mutuwa mai yanka 'kauna shikenan sun kashe min ita wayyo ni na'eema karki tafi ki barni ke kadai na mallaka, na shiga uku na lalace wallahi ita kenan gareni_ Abba ne yayi k'arfi halin rik'o umma hajara yace kiyi takwali hajara Allah da yabaki na'eema shi, ya k'arbi abar sa halin yanzu na'eema tafi bu'katar addu'a ki fiye da wannan kukan da ki ke yi mata umma hajara ta'kara fashewa da sabon kuka had'e da chakume rigar Abba, duk yadda Abba yaso tadaina kuka abin yaci turu sai kawai yasaka mata ido saboda abin kuka ne yasame ta dole tayi kuka. Ba'a d'auki dogon lokacin ba aka fito da gawar na'eema aka sakata cikin _ambulance_ kaitsaye aka nufi gida da ita yayida Amar baisan duniyar da yake ba saboda har yanzu yana ciki _coma_ in kadebi zuciya sa babu abinda yake motsi a jikinsa hatta da numfashi sa ta _oxygen_ yake fita lokacin da aka eso da gawar na'eema, raheela soma tayi da kyar aka samu ta farfad'o sai faman kuka takeyi gaba d'aya gidan ya kachame da ihu had'e da kukan mata raheela na kwance a jikin kaka idanu ta jajir kamar mai ciwo ido _Apollo_ muryar ta duk ta dishe saboda kuka, tace shikenan kaka yaya na'eema ta tafi ta barmu kaka tace duk mai rai mamaci ne raheela kowa lokacin sa yake jira kiyi mata addu'a shine zai nuna cewa 'kaunarta' Raheela ta fashe da kuka abin gwanin ban tausayi, cikin muryar kuka tace _ya Allah kayi mata rahama ka had'a ta da haske kabari kabata iko amsa tambayoyi cikin sauki_ kaka ta goge hawaye had'e da cewa *Ameen* Misali 'karfe *10:00am* akayi _jana'izza_ na'eema aka kata gidanta na gaskiya umma hajara tana gani anfita da gawar na'eema ta yanke jiki tafad'i saida aka shek'a mata robar ruwan _faro_ biyu sannan tadawo haiyaci ta ranar umma hajara 'yar 'karamar hauka tayi. Sai da yamma raheela tasamu ta bud'e wayar ta, ta kira Ayshat _ringing_ d'aya zuwa biyu ta d'auka raheela lafiya ki ke tun jiya nake kiran wayar ki arufe naje gidanku maigadi yace kun fita Ku duka"? Raheela ta sauke ajiyar zuciya daga bisani ta 'korowa Ayshat abunda ke faruwa Ayshat ta rud'e sosai, daga bisani tace _Allah yajik'an na'eema yasa ta huta shi kuma yaa Amar Allah yabashi lafiya_ *Ameen* _besty_ na gode Allah yabada lada. Ayashat tacigaba da cewa insha Allah gobe zan zo nayi wa su umma _ta'aziyya_ to besty sai kin zo sukayi sallama raheela ta kashe waya. *BAYAN KWANA UKU* A yau ne na'eema ta cika kwana uku da rasuwa akayi addu'a uku 'yan uwa na nesa da na kusa suka watsi gidan yayi saura daga umma hajara sai 'yan uwa ta na jini da yake aunty amarya a _hospital_ take yini kwana kadai yake dawowa da ita gida kaka da mami kuma suna _part_ d'in su wannan ne yabawa umma hajara furtawa 'yan uwa ta abunda ke ci mata tuwo a kwarya ta kalle aunty Asabe idanu ta na tsiyaya hawaye tace........ [30/07 8:49 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 7⃣8⃣ Burin Amar da raheela ya cika sun rabani da na'eema, dakata hajara aunty asabe ce ta katsi ta haba hajara kada mutuwa na'eema ta zauta ki mana ta yaya za ki danganta mutuwar na'eema da Amar da raheela bayan kowa yasan _accident_ sukayi har yanzu Amar yana ciki halin 'kila wa 'kala. Umma hajara ta fayyace majina da gefen hijab d'inta, ta kwashe labari yadda akayi Amar ya aure na'eema har izuwa abunda yafaru ta sanarda 'yan uwa ta aunty asabe tayi salati had'e da tafa hannaye daga bisani tace lallai hajara kinyi sake, d'an zaki ya girma ke wayagaya miki ana dogaro da aikin boka d'aya ae ba lalle bane koda yaushe aikin boka duguzuu yake tasiri, shikenan kinyi tutar babu baki ga tsuntsu baki ga tarko 'yar da ki ke tunani in ubanta ya mutu ki gaji dukiya ta mutu a yanzu bakida martaba a gidanan kodai ki tashi tsaye chak kiyi tsayin daka kiyi amfani da damarki tayi miki amfani ko kuma ki zauna garin kallon ruwa k'wado yayi miki 'kafa ta'karasa magana had'e da kyabe baki. Suwaiba ta karbe zance ta hanyar cewa ae kema aunty hajara da laifi ki duk abunda za kayi duniya karka nemi ka salwata rayuwa wani da tun farko kince asaka asirin a tsohon kabari da yanzu raheela ta haukace, don haka qaiqayi ne ya komawa mashek'iya a maimako raheela ta mutu sai 'yar ki na'eema ta mutu da za ki d'auki shawara ta da nace ki zubarda makamai ki kada garin gyaran gira arasa ido domin naga alama a wannan tafiyar bakida Sa'a. Tun lokacin da tafara magana hajara da asabe suke aika mata mugun kallo, aunty asabe tace ke suwaiba duk wannan kwana-kwana da ki keyi kifito filin kifad'a mana cewa kina baki cikin da hajara ba wai ki ce ta zubarda makamai ba ko don bakece aka cuta ba"? Don na fad'a mata gaskiya shine za ki danganta ni da 'yar bak'i ciki to ni bana mata bak'i ciki ina dai tausayi muguwa hanya da ki ke yun'kuri jefa ki. Umma hajara ta zuburo tamkar za ta daki suwaiba tace lalle suwaiba bakya 'kauna ta in har ke ba za ki tayani d'aukar famsa abunda akayi min to ki zuba ido kisha kallo ba ruwanki. Haka aunty asabe tacigaba da zuga umma hajara yayida umma ta hau ta zaune bisa ga gurguwa shawara da tabata. Dr Abbas na zaune a office d'in sa daddy da Abba suna zaune yana musu bayani dangane da ciwo Amar gaskiya Alhaji da za Ku d'auki shawara ta da nace kunfita da Amar kasar waje domin anan bamuda wasu kwarari kayan aiki yau kwana sa biyar kenan ko d'an yatsa sa bai motsi ba hatta da numfashi ta _oxygen_ yake shak'ar sa ga kuma kariya 'kafa da hannu. Daddy yasauke ajiyar zuciya yace Dr kana gani wane kasa yadace mu fita da shi"? _Germany_ ita ce da yadace Ku kai shi _Co's_ suna da likitoci kwararu daddy yace mu gode sosai likita. _BAYAN KWANA BIYU_ Bayan kwana biyu aka wuce da Amar _Germany_ Raheela na kwance a falon kaka kallon d'aya za ka yi mata ka gano rama da tayi yaya hafsat ce tashigo ta d'an zaro ido had'e da cewa wai raheela har yanzu kina nan a kwance baki shirya ba"? Raheela ta mik'e zaune tace na shirya yaya hafsat kawai na d'an kwanta ne kafin _driver_ yazo _okay_ kifito da kayan naki ga _driver_ nan yazo raheela ta mik'e ta shiga d'aki tafito da _trolley_ d'in ta kaka na biye da ita kaka tace Dan Allah hafsat ki saka ido akan raheela tun lokacin da akayi rasuwa nan bataso cin abincin Yaya hafsat ta yi murmushi tace zan kula da ita _insha Allahu_ kaka da haka sukayi sallama da sauran jama'a gidan suka d'auki hanyar _Abuja_ Tun lokacin da raheela ta koma _school_ ta dawo _so silent_ duk da yaya hafsat tana kula da ita sosai. *GERMANY* A _Germany_ kuma Satin Amar d'aya yafarfad'o har yana iya magana, yana dawowa haiyaci shi ya tambayi na'eema Abba ya kalle shi cikin tausayi yace na'eema ta ji sauki Amar ya lumshe idanu shi saida ya share tsawon wata d'aya a _Germany_ sannan suka dawo gida _Nigeria_ a lokacin yana iya tafiya da 'kafafu sa. _BAYAN 1 HOURS_ Bayan awa d'aya da dira Amar _Nigeria_ yana zaune a falon daddy yace daddy tun lokacin da nadawo banga na'eema ba ko batasan nadawo bane"? Daddy yayi shiru yakasa bashi amsa Amar yace daddy kayi baka bani amsa ba"? Tun lokacin da ina _Germany_ in na tuna da na'eema sai na tsinci kaina da fad'uwar gaba Dan Allah daddy kafad'a mini ina na'eema"? Har daddy ya bude baki yabashi amsa sai ga Abba da umma hajara sun shigo, umma hajara ta tabe baki tace banga amfani boye masa da Ku keyi ba domin ba shi zai sanya 'yata tadawo duniya ba kai Amar duk wani boye-boye ya'kare na'eema ta mutu. A lokaci d'aya tsnanani tsoro had'e da tashin hankali suka ziyaraci Amar wani mashahuri gumi ya lullube shi numfashi sa yafara Kai da kawo daga bisani numfashi nasa ya tsaya chak ya sulale 'kasa a _some_....... Jeeddah Aliyu🌹 [01/08 9:38 am] Jeeddah Aliyu🌹: [31/07 5:17 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 7⃣9⃣ Da sauri Daddy yad'ago shi yana girgiza shi, had'e da kiran sunan shi, mami ta mi'ke da gudu tashiga _kitchen_ ta d'auko robar ruwan _Mr. V_ mai matu'kar sanyi ta mi'kawa Abba ya kwarawa Amar nan take Amar yasaki katuwar ajiyar zuciya, yasoma kallon mutane falon daga bisani yafashe da kuka cikin murya kuka yace _Allah sarki na'eema kin tafi a lokacin da nakeda 'kudiri nuna miki tsantsan 'kulawa kin tafi a lokacin da nasha alwashi danne zuciya ta, da tacigaba da zama da ke har 'karshen rayuwa ta "Allah yagarfata miki na'eema yasa kin huta_ yana k'arasa magana had'e da fashe da wani Sabon kuka Abba ya rungume shi yana bubuga bayan sa cikin sigar rarrashi yace hakuri za kayi Amar _duk mai rai mamaci ne tsakani mu da na'eema sai addu'a_ Abba ya taya shi mik'ewa yaraka shi d'akin shi yace ka kwanta ka huta Amar karka saka damuwa a ranka ko don yanayi jikin ka Amar yad'aga kan shi ha'de da cewa na gode Abba. Umma hajara nagani Abba yafita da Amar sai tasami damar yada maganganu maras asali balle kan gado bakinta na fitarda kunfa bala'i da masifa don tsabar mugunta an kashe mini 'ya, to wallahi ahir d'in Ku ashirye nake duk Wanda yakeda sa hannu a mutuwa ta. A fusace mami ta mik'e ta nuna umma hajara da yatsa tace na fahimci cewa hajara bakida hankali in banda hauka da dabbaci irin naki waye ya kashe miki 'ya anan"? Amar shine ya kashe na'eema saboda baya sonta ya tsane ta, shiyasa ya kifarda mota 'yata ta mutu. Daddy da Mami suka d'auki kalma shahada mami tace anyya hajara za ki ga Annabi kuwa"? Tsabar jahilci da rashin takwali yana 'kokari jefa ki mahalaka, in banda jahilci kina _musulma_ amma ace bakisan da cewa Allah {S.W.T} shi yake rayawa kuma shi yake kashewa tir da wannan da'ki'kici naki yi maza kifita ki bamu wuri tun kafin nayi miki abinda baki tab'a tunani ba Allah yashirye ki yasa ki gane gaskiya. Umma hajara taja tsoki had'e da cewa za ka Ku ga abinda zai biyo baya tafice daga falon Mami tace mu ga alkhairi ta koma ta zauna tajuya wurin Daddy da ke dafe da goshi tace Alhaji kana ji abunda wannan jarabanbiya matar tafito da shi"? Daddy yasauke numfashi yace naji fateema ha'kuri za kiyi kidaina biye mata watakila zafin mutuwar na'eema ne yatab'a ta mami ta tabe baki had'e da cewa Allah ya kyauta. _ABUJA_ Raheela da Ayshat sun fito daga _lecture_ wayar raheela tayi _ringing_ tafito da ita daga _handbag_ gani Wanda yakira yasa ta ja tsoki had'e da bata fuska kamar za tayi kuka, Ayshat ta kalle tace miye haka kin wani 'bata fuska sai kace wance tasha mad'aci"? Bari kawai _besty_ na had'u da 'karfe 'kafa gaba d'aya _guy_ nan ya takurani ya hanani sukuni _I don't known what's to do_ Ayshat ta kyakyale da dariya tace kina nufi suleiman"? Shine _besty_ so yake da k'arfi da yaji ya cusa mini sonshi' Yatsine fuska Ayshat tayi daga bisani tace nifa banga illah Suleiman ba' Nima bance miki yanada illah ba kawai dai yayi min girma Ayshat tak'ara kyakyalewa da dariya tace kin shiga uku raheela mutum yana haukan sonki ke kuma kina masa sharri. Raheela tayi dariya tace Suleiman yafiye naci, ko don wannan naci nasa dole na saurare shi. _WANENE SULEIMAN_?? Suleiman haifafe garin katsina ne shekuru sa na haihuwa ba za su haura 37 ba ma'akaci banki ne unguwar su d'aya da yaya hafsat gidaje biyu ne a tsakanin s tun lokacin da ya 'kyala ido akan raheela yanace mata shi dole sonta yakeyi tun raheela bata kulashi har tadawo tana saurare shi. _KADUNA_ Bayan sati biyu da dawowar Amar daga _Germany_ ya ji sauki sosai,don haka yau yahad'a kayan shi zai koma _Abuja_ zaune yake a falon kaka yace kaka na zo ne nayi miki sallama zan koma a bakin aikina. Kaka tace to Amar Allah yakai ka lafiya ka kula da tu'ki karkayi mugun gudu nan da ka keyi Amar yayi murmushi, kaka tace bara na kawo maka sak'on raheela ras gabanshi yafad'i tun dawowar shi yakeso ya tambayi raheela sakamako rashin ganinta da yayi amma yana tsoro amsar da za'a bashi.... [01/08 9:36 am] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 8⃣0⃣ Har kaka tafito daga d'aki baisaniba ya zurfafa a tunani haske zuciyarsa raheela, saida kaka ta kira sunanshi da k'arfi sannan yadawo daga dukiya da yalula cikin tausayawa kaka tace Amar yakamata ka rage tunani a matsayin ka na likita kasan irin illah da yake haifarwa Amar yad'an Sosa kai yace na gode da wannan shawara taki kaka, ina sak'o yake"? Kaka ta mik'e masa katuwar leda bak'a da sauri Amar yatoshe hanci had'e da cewa wari daddawa nakeji kaka me raheela za tayi da _daddawa_? Kaka ta galla masa harara tace to miye kuma na toshe hanci? Banaso wari daddawa kaka' Kana nufi kenan ba za ka, kai mata _sak'o_ ba"? Leda _daddawa da garin kuka_ na hafsat ne ledar aya mai sikari da garin d'an wake da kuma yaji na raheela ne kasan raheela na matukar son 'dan wake' Amar ya tabe baki yace kaka kina sagarta raheela da yawa har wani _aya mai sikari_ ki keyi Mata Kaka tace ina ruwanka kadai sak'o ne na baka in kuma ba za kai mata ba ka bani kayana Amar ya mik'e yace ni na tafi kaka saboda na fahimci so ki keyi mu yi fad'a kafin na tafi ni kuma banaso yin fad'a da ke' Kaka tayi murmushi ta bishi da _addu'ar fatan alkhairi_ _ABUJA_ Raheela na zaune a falon tana kallo jabeer _first born_ d'in yaya hafsat yashigo ya zauna kusa da ita yayi 'kasa da murya yace aunty raheela _uncle Suleiman_ ya zo raheela tayi murmushi had'e da cewa _okay_ kace ina zuwa tashiga d'akin da ya kasance nata tayi _simple make up_ tafesa turare _eternity for women_ tafice zuwa _compound_ tun kafin tak'araso yafara wanke ta da murmushi, barka da fitowa _my heartbeat_ Yauwa ina wuni"? Lafiya amma ba qalau _my heartbeat_ Raheela ta d'an zaro ido tace me ke faruwa ne suleiman"? Ya lumshe idanu raheela duk lokacin da ki ka kirani da suleiman sai naji wani sabon, shauk'i sonki yana 'kara samu masauki a cikin zuciyata ina sonki raheela amma ke Sam bakida damu da ni ba Raheela tayi murmushi tace dad'i da kai kenan a _suleiman_ kullum 'korafi ka guda d'aya ne ban damu da kai ba da bakada muhalli a zuciyata da ba zan dinga sauraro ka ba' _suleiman_ ya washe hak'ora kamar gonar auduga, yace in kuwa haka ne _my heartbeat_ ki amince iyayye na suje gidanku domin asan da zamana. Raheela tayi dariya had'e da cewa suleiman zumudi duka-duka wata d'aya kachal da had'uwar mu komai zumudi ka, ka jira har mu gama fahimtar juna koh"? Wane irin fahimta raheela"? Ni fa na fahimce ki sai in kece baki fahimce ni ba in har ba so ki ke nayi miki kuka ba raheela ki bani wannan damar _please_ yadda yayi magana ya ba raheela dariya batasan lokacin da ta kyakyale da dariya ba da yake _suleiman_ shashasha ne akan mace kawai sai yataya raheela dariya. Dai-dai lokacin da _Dr Amar matawalle_ yadanno hanci motarsa a farfajiya gidan yaya hafsat tuni idanu sa sun hasko masa raheela wani irin masifafe 'kishinta ya lullube shi, a zuciyarsa yace wane 'kato banza ne raheela take tare da shi"? Mtwww.... yaja tsoki lalle yarinya tasamu sake a gidanan shiyasa ta kafa samsani fira da katti da wannan zance zuci yayi _parking_ yafito daga mota ko kallon wurin da suke tsaye baiyi ba kaitsaye yashige cikin gida. Raheela ta katsi da dariya da takeyi ta bishi da kallon mamaki yaushe wannan mugu yadawo ne? Amma wannan _brother_ d'in ki ne koh"? Kafin taba Suleiman amsa saida ta yatsine fuska daga bisani tace ni ban had'a komai da shi ba Suleiman ya kyakyale da dariya yace kai _my heartbeat_ yanzu duk wannan kama da ki ka yi da shi za ki ce baki had'a komai da shi ba kallon d'aya za'ayi mishi a gano cewa yayanki ne don kunyi masifar kama saidai kinfi shi kyau. Raheela tayi dariya tace to na gode zan shiga gida, Suleiman ya marairaice murya yace tun yanzu _my heartbeat_ wallahi ban gaji da gani wannan _beautiful face na ki ba_ raheela tayi murmushi had'e da cewa gobe ma rana ce za ka iya dawowa, suleiman yasaki murmushi jin dad'i yace na gode da wannan damar da ki ka bani _my heartbeat_ Raheela tace _you are highly welcome_ Amar yayi sallama yashiga falon da gudu fahad da jabeer suka rungume shi _uncle oyoyo_ fuskar Amar d'auke da murmushi yace ina yaya hafsat"? Fahad yace tana _bedroom_ bara na kira ta Amar yanemi kujera ya zauna yaya hafsat tafito tana rik'e da kausar tace barka da zuwa likita Amar yayi murmushi had'e da cewa yauwa babban yaya da fatar na same Ku lafiya"? Lafiya qalau ya 'karfi jiki? Jiki _Alhamdullah_ raheela tayi sallama tashigo yaya hafsat ce ta amsa mata yayida Amar ya watsa mata mugun kallo Wanda ya hadasa mata fad'uwar gaba....... Jeeddah Aliyu🌹 [01/08 8:34 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [01/08 12:53 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 8⃣1⃣ Raheela tanemi kusa da yaya hafsat ta zauna, tayi kamar bata ga Amar ba sai fama _operating_ d'in wayar ta takeyi yaya hafsat takasa hak'uri tace raheela baki ga Amar bane"? Na ganshi mana ae mu gaisa a 'kofar gida Amar ya bud'e baki da hanci yana kallon raheela, daga bisani ya kawarda fuskar sa ta mik'e ta nufi d'akinta Amar yabita da kallon yayida yaya hafsat take kallon shi cikin tausayawa tace Amar Cikin tsanani jin kunya Amar yajuyo yace _Na'am_ yaya hafsat" Na fahimci cewa raheela ita ce farin ciki ka, me zai hana kabani dama na sanarda kaka tayi magana da su Daddy, su a aura maka ita domin samu kwanciyar hankali ka tunda _addini_ bai hana ba na tabbata suma za suyi farin ciki da jin raheela za ta maye gurbi 'yar uwa taa. Amar yasauke gwaron numfashi cikin murya mai matukar ban tausayi yafara magana, tabbas yaya hafsat ina masifar son raheela amma a yanzu na ha'kura da ita saboda banaso na zamo sila kawo sabani a zuri'ar mu ita kanta raheela bata sona _she hate me, so much_ Yaya hafsat tayi ajiyar zuciya tace raheela ba matsala bace ni nafi kallon umma hajara a matsayin babbar matsala da za ta kawo cikas tsakani ka da raheela, amma kabar komai a hannu na _I will try my best_ nagani burin ka yacika Amar yayi murmushi jin dad'i yace na gode yaya hafsat da wannan taimako naki agareni yaya hafsat tace amma da cewa kayi ka ha'kura da ita"? Fad'a kawai nayi yaya hafsat son raheela ya riga yayi min illah, ko yanzu nan da na shigo naganta da wani shirgege 'kato baki ga yadda zuciyata ta dinga tafarfasa ba yaya hafsat ta kyakyale da dariya tace to kayi 'kok'ari ka siye zuciyata, tadaina kula shirgege 'kato Murmushi Amar yayi yace zuciyar raheela ce tamkar dutsi shigar ta yanada matukar wahala. Karka zama matsoraci Amar ni a ganina babu zuciyar da baza ka iya ratsawa don haka kayi amfani da damar ka ta d'an namiji ka mallaki zuciyar raheela shikenan yaya hafsat zan gwada amma Dan Allah kidaina barinta tana fita banaso naganta da kowa yaya hafsat ta tabe baki had'e da cewa kaji da shi. Da Wannan zance Amar yayi sallama da yaya hafsat yawuce gidanshi katsaye _bathroom_ yanufa yasakewa jikinsa _shower_ bayan yafito daga _bathroom_ yasaka _pajamas_ yafeshe jikinsa da turare _pure blue_ ya haye gado ya lumshe idanu shi yasoma tunani irin rayuwa da yayi da na'eema _Allah sarki my na'eema kintafi a dai-dai lokacin da nakeda buri kyautata miki_ ya sauke gwaro numfashi yajuya ya janyo _pillow_ ya rungume a 'kirjishi yayida zuciyarsa take hasko masa kamanu raheela, ya mik'a hannu bisa _bedside_ yad'auki wayarsa yayi _dialling_ number raheela Kwance take takasa baccin sai faman juyi takeyi bisa gado jin _ringing_ d'in wayarta yasa taja tsoki baiyane tace wash Suleiman yana son ya kashe ni har da dare ba zai barni na huta ba"? Yaa Amar tafad'a had'e da zare ido me yaa Amar yake nema a wurina a dare nan"? Tad'ago idanu ta, ta kalli _agogo 10:30pm_ yayida wayar tacigaba da _ringing_ kamar ba zata d'auka ba sai kuma ta chanza shawara tayi _picking_ A sanyaye tace _hello_ yasaki ajiyar zuciya sautin yasauka a dodo kunne raheela, batasan lokacin da ta lumshe idanu ta ba tsawon da'ki'ka uku suka d'auka ba Wanda yace komai gani shiru yayi yawa yasa raheela tace in baka abin cewa zan ajiye waya, Amar y marairaice murya kamar zai yi kuka yace _raheelaaa_ yadda yaja sunan nata ya haddasawa tsigar jikinta tashi amma tauri rai irin na raheela sai kawai ta fuske kamar bataji komai ba tace _ya akayi ne Mr hero_? _Bakida kirki raheela ina matsayin yayanki amma bakya girmamani na share tsawon wata d'aya a Germany ina jinya baki tab'a daga waya ki, kirani ba nadawo kuma kin kasa yi mini sannu me nayi miki raheela da ki ke nuna mini zazzafa 'kiyayya_? Ba kayi mini komai ba yaa Amar kawai dai banada ra'ayi magana da kai banaso kowace ala'ka tak'ara shiga tsakani mu ina mai baka shawara kafita hanya ta saboda na tsane ka bana sonka yaa Amar. Da sauri Amar ya katsi wayar domin ba zai iya cigaba da juri jin mumuna kalaman raheela ba mik'e zaune yayi tagumi yasoma zance zuci ya zanyi da sonki raheela? Ko za ki yanka ni raheela bazan daina sonki ba. Haka Amar yacigaba da sintiri a gidan yaya hafsat da raheela taji muryar sai ta shige d'aki ta murza _key_ ba za fito ba har sai yatafi in kuma ya kira ta da waya tak'i d'agawa damuwa ta taro tayiwa Amar yawa duk yabi ya rame ko lokacin da yayi hatsari baiyi ramar da yayi a yanzu ba gani yadda yake ramewa kada ciwo zuciya ko hawan jini Yakama shi yasa yaya hafsat ta yanke shawara yiwa raheela magana raheela magana Amar ce nakeso muyi raheela ta bata fuska had'e da cewa maganar yaa Amar kuma"? [01/08 8:34 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 8⃣2⃣ Kwarai kuwa maganar Amar, raheela yakamata ace zuwa yanzu kin amince da soyayya da Amar yakeyi miki,ki tausayawa d'an uwanki ki dubi yadda Amar yarame yafita haiyaci sa duk a dalilin son da yakeyi miki ina 'kule da ke duk lokacin da yazo gidanan sai ki shige d'aki ki boye kuma kinsan saboda ke yake sintiri a gidanan. Raheela tayi shiru tana kallon yaya hafsat kamar yau ne tafara ganinta daga bisani tace haba yaya hafsat kwata-kwata _watani_ hudu da mutuwa yaya na'eema ace anfara yi mini maganar yaa Amar wannan wane irin gwad'o ne"? Koda ace inaso yaa Amar ba zan iya aure shi ba saboda ```mijin 'yar uwa taa ``` ne nikan ba zan iya wannan abin kunya ba haka kawai ina zama-zama na yaa Amar yanaso yad'auko abunda yafi k'arfi na yanufo ni, da shi nace bana sonshi dole ne. Yaya hafsat ta tsurawa raheela ido tana mata kallon mamaki daga bisani tace raheela kada ki jahilci abinda baki saniba addini ya halattawa Amar aure ki babu inda akayi hani da ```k'anwa bata aure mijin yaya taa ``` don haka kuskure ne ki dinga daganta hakan da _abin kunya_ raheela ta share hawaye ta, tace bazan boye miki ba yaya hafsat banaso yaa Amar kuma ina rok'o ki da ki rufe wannan zance anan banaso su ```daddy su San da wannan zance ``` Yaya hafsat tayi murmushi tace shikenan raheela insha Allahu ba zan 'kara yi miki zance Amar amma inaso kisani Amar yaso ki tun kafin kinsan ```wacece ke ``` Kuma ina da ya'kini cewa zai cigaba da sonki har karshen rayuwa sa. Raheela ta sunkuyarda kai 'kasa tana sharar hawaye yayida yaya hafsat ta mik'e tafice daga falon tabar raheela zaune tana kuka. _WASHE GARI_ Bayan raheela taje _school_ ta zayanewa Ayshat yadda sukayi da yaya hafsat, yanzu fisibillahi in naso yaa Amar ae ban yiwa yaya na'eema adalci ba kuma tun tana raye nayi mata alk'awali bazan tab'a son mijin ta ba shine yanzu don bata raye sai na k'arya alk'awali gaskiya ni bazan tab'a iya cin amanar yaya na'eema. Dad'i na da ke raheela shirme wane irin cin amana ae ita na'eema tun tana raye tasan ba ita yaa Amar yake so ba ke yakeso raheela, 'kaddara ce ta had'a su kuma a yanzu mutuwa ta raba su wallahi yaa Amar yana matuk'ar bani tausayi ko jiya da yaje gida na yana yi mini _k'orafi_ akan irin wulak'anci da ki ke yi masa saida ya zubarda hawaye _kai so masifa ne_ Cikin bacin rai raheela tace dallah dakata malama ke ki ka bashi izzini yaje gidanki koh"? Ayshat ta galla mata harara had'e da cewa gida na yaje ba gidanki ba don haka ba ruwanki kuma ina tausayi miki ranarda za ki fad'a a tarko son yaa Amar na tabbata har, hauka sai kinyi. Raheela taja tsoki tace ni _raheela abdullah matawalle_ naso yaa Amar _god forbid_ ko a mafalki bazan tab'a son yaa Amar ba don haka ki rubuta ki ajiye duk ranarda naso yaa Amar ki sakani a gaba kiyi mini dariya iya son ranki. Ayshat ta kyakyale da dariya tace kidaina cika baki raheela _shi so baya neman izzini shiga zuciyar d'an-Adam kawai yakeyi so cuta ne raheela in yasami muhalli a zuciya ba 'karama barna yakeyi ba_ Ina ruwa na da zaman shi cuta duk Wanda ki ka ga ya cutar shi yayi sake ni nan zuciyata a datsi take bana tunani ina cikin _jinsi_ da so yake cutarwa. Ayshat ta tabe baki had'e da cewa chan ta matsi miki. ```BAYAN SATI D'AYA``` Raheela tadawo daga _school_ a gajiye tashiga falon ta tararda yaya hafsat da su jabeer zaune tun kafin ta zauna yaya hafsat tace ke kadai mu ke jira raheela za mu tafi Kaduna yanzu nan raheela ta zaro ido tace Kaduna kuma lafiya za mu tafi Kaduna da yamma nan"? Lafiya qalau _family meeting_ za'ayi ba yadda raheela ta iya dole ta shirya suka d'auki hanyar Kaduna. ```KADUNA``` A lokacin da su raheela suka eso falon Daddy a cike yake da 'yan uwa suna had'a ido da Amar ta murgud'a masa baki shi kuma yayi murmushi suka bi sahu mutane falon suka nemi wuri suka zauna yayida abdul haleem yabud'e taro da _addu'a had'e yiwa marigayiya na'eema addu'a_ Daga bisani daddy yafara magana dalilin da yasa muka taro anan shine muna so gobe _jama'a_ insha Allah za mu cikawa marigayiya na'eema wasiya da tabar mana. A zuciya raheela tace _Allah sarki yaya na'eema harda wasiya tabari_ Yayida daddy yacigaba da ce wa wasiya da na'eema tabari shine had'a Amar da raheela aure tun kafin daddy yadasa aya Amar da raheela da kuma uwar gaiyya umma hajara a lokacin d'aya suka mik'e tsaye kowane su da yanayi tashin hankali sa..... Jeeddah Aliyu🌹 [02/08 7:32 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [02/08 11:14 am] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 8⃣3⃣ Umma hajara ta bi mutane falon da k'as'kantace kallon daga bisani tasoma tafa hannaye, tace lallai mutane gidanan kun kware a fagge na cin amana da zalunci abin kunya gaba Ku ka bashi ba baya ba to na rantsi da Allah ba zan amince kowane d'a mace ya tozartani a ido duniya ba wannan kwamacala har ina 'kanwa ta aure mijin yayarta dama ni nasan akwai mak'ark'ashiya a mutuwa na'eema haka umma hajara tacigaba da zubda ruwan rashin mutunci kowa ya zuba mata ido saida tagaji don kanta tayi shiru. Abba ya mik'e tsaye cikin kwanciyar hankali ya nuna mata kofa da hannu shi yace tunda kin gama ae sai kifita ko"? Umma hajara sai faman huci takeyi kamar kububuwa tace kaji tsoron Allah Abdullah kana nuna banbanci a tsakani 'ya'ya ka kafifita raheela akan saura 'ya'ya ka tun na'eema tana raye kafi son raheela akanta yanzu kuma bata raye kafito da wani sabon salon cin amana ka d'auki mijinta sukutun kabawa raheela wannan wace irin 'kiyayya ake nuna min a gidanan"? tak'arasa zance ta had'e da rushewa da kuka Abba yafisgo hannu ta da k'arfi ya cilla ta waje yace kifita ki ba mu wuri ke kin manta da irin zalunci ke da 'yarki Ku ka yiwa Amar wallahi koda ace Amar bayaso raheela na'eema ta mutu sai na aura masa ita ballatana ita ce zabi sa kai Amar a matsayi na na mahaifi raheela na mallaka maka ita kyauta' Raheela da tayi mutuwa tsaye hawaye kawai ke fita daga idanu ta sakamako jin furunci Abba na 'karshe yasa ta daka tsalle tayi fad'uwa 'yan bori, tace wayyo, wayyo jama'a ku taimake ni Ku kawo mini agaji zuri'ar Abdulrazaq matawalle sun had'e mini ka za su kassara rayuwa ta wallahi banaso yaa Amar, ni bazan aure ```MIJIN 'YAR UWA TAA ``` da na aure yaa Amar gara na 'kare rayuwa ta a _prison_ kai, kai ina wallahi ba zan aure yaa Amar ba ke kuma umma hajara da ki ke cewa Abba yafi sona ba gaskiya bane yafi so kowa akaina Abba ya tsane ni baya sona aunty amarya ta mik'e tsaye ta wanke raheela da mari a maimako raheela tayi shiru sai ma tak'ara 'kaimi tacigaba da zuba sai kace zautata na gwance yadda Ku ka yi mini taro dangi ku taso kuyi ta duka na sai na mutu da na aure yaa Amar. Daddy da yaga abin na raheela yafara yawa ya mik'e ya kamota yace raheela kiyi hak'uri ki bamu had'in kai mu cikawa 'yar uwarki alk'awali da muka d'auka mata da ace Amar yana da wata illah bazan amince a aure miki shi ba, raheela tak'ara fashewa da kuka tace shikenan 'karshe na yazo ya Allah ka ji'kaina ba don na mutu ba domin na tabbata ko mutuwa nayi duk gidanan ba wanda zayi min _addu'a_ saboda ba su sona tajuya wurin kaka tace kaka kina kallo za'a had'e ni da mugu maras tausayi da imani abdulhaleem yadaka mata tsawa ke dallah ki yiwa mutane shiru In banda ```'KADDARA SO ``` me yaa Amar zayi da ke mahaukaciya kawai fitsarariya Dallah dakata malam nazee ne ya takawa abdulhaleem birki cikin zafin rai da konar zuciya yace kadaina yi mata _shouting_ ka barta taji da zafi d'aya mana da sauri raheela tafisge daga rik'o da daddy yayi mata ta nufi wurin Nazee ta fad'a jikinsa tace dan Allah yaya nazee ka taimake ni karka bari a aure mini yaa Amar _please yaya Nazee help me I don't love him I really hate him I don't wants to be with him any more_ Hawaye suka zubo daga idanu nazee yace _calm down raheela_ da ina da yadda zanyi na rabaki da aure nan da nayi kiyi ha'kuri kawai amma wallahi ancuce ki aure dole sai kace muna 'kauye Mami ta gallawa Nazee harara tace ka fa nazeer bakada mutunci a maimako ka rarrashe ta sai ka buge da zugata Ni fa mami ba zugata nakeyi ba gaskiya ce nafad'a a wannan karo yaya hafsat ce ta karbe zance ta hanyar cewa dallah ka rufewa mutane baki munafuki kawai da bayaso alkhairi Daddy yadaka masu tsawa yace miye haka banaso shashaci Abba yace kyale su kawai yaya kowa ya fad'i albarkaci bakin sa insha Allah gobe Raheela ta zama mallakin Amar Sai lokacin kaka tayi magana tace ae tun farko laifi Amar ne da baisan yadda ake bayyana so ba barshi dai da d'an banza fad'i rai da miskilanci tsiya ni ba ruwa na chan ta matsi muku kaka tak'arasa zance ta had'e da ficewa daga falon yayida Abba da daddy suka Mara mata baya. Raheela tajuya wurin da Amar yake zaune ya wani aza 'kafa bisa 'kafa yana tauna _chin gum_ sai faman danna waya yakeyi hankali sa kwance' Raheela tace yaya Nazee kalli yadda wannan _wicket man_ d'in ya hard'e 'kafafu yana kallon mutane a wulaqance Allah kadai yasan irin mugun tanadi da yatanada min a ciki zuciyarsa. Nazee yace karki damu Allah yafishi amma yadda tsofafi nan suka cika falon nan tabbas mai hanaki zama matar yaa Amar sai Allah zo muje na baki wata kyakyawa shawara da sauri Mami tace kai nazeer ka kiyayye ni wace irin shawara ce za ka bata da mu baza mu bata ba"? Amar yaja wawa tsoki yafice zuciyarsa na tafarfasa jin yakeyi kamar ya rufe nazee da duka yana fita nazee yaja hannu raheela suka fice daga falon...... [02/08 7:31 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 8⃣4⃣ Suna fitowa suka hango Amar cikin mota zai fita raheela ta bi motar da kallon takaici, kaitsaye _part_ d'in kaka suka shiga raheela tafad'a jikin kaka tafashe da kuka tace Dan Allah karki bari a had'ani da yaa Amar wallahi banaso shi na tsane shi kaka tace haba raheela miyasa bakida han'kuri da yafiya"? Amar d'an uwanki ne yana matukar sonki na tabbata wata rana za ki gano alkhairi da yake tartare da Amar Raheela ta zare jikinta daga jikin kaka a zuciyata tace ita ma wannan Tsoho tana bayan yaa Amar, ta mik'e tsaye ta kalli kaka tayi murmushi ta kuma share hawaye ta tace shikenan kaka a yanzu banida mafita ina kallo zan kasance matar yaa Amar to amma kuma ba komai ni nasan yadda zanyi don na k'arawa zaman aure mu armashi abin mamaki ni da yaa Amar za mu rayu a gida d'aya kuma a matsayin ma'aurata ta 'karasa magana had'e da kyakyalewa da dariya ta juya tashiga _bedroom_ Nazee yayi tsalle ya haye kujera ya zaro ido yace anyya kaka raheela bata zare ba kuwa"? Kaka ta watsa masa mugun kallo in har ta zare ae da 'kari sa hannu ka domin Kaine munafuki da yake 'kara zugata. Haba kaka ya za'ayi acuci yarinya sannan kuma kuce ba za'a tausaya mata ba' Ba Wanda ya cuci raheela sai anan gaba za Ku gano cewa gata akayi mata Aure Dole ba gata bane kaka da gata ne ke me yahana ayi miki naga kema aure soyayya ki kayi sai raheela ce za Ku yiwa dole don kawai ku farantawa yaa Amar rai' Lallai nazeeru wuyan ka yayi kauri ya isa yanka har ni za ka kalle kace nayi aure _soyayya_ ? _Eh nafada aure soyayya ki kayi ae ba karya na fad'a ba ke ni daga yau mu raba jam'iyya ni da ke_ Kaka tayi murmushi tace ae kuwa da na huta da halinka tashi maza kafita mini daga falon kuma daga yau karna 'kara gani 'kafarka anan. Matukar raheela tana _side_ d'inan kindinga gani 'kafata kenan. Ja'iri banza marar zuciya tsanani dad'ewa raheela a gidanan gobe saidai in bin ta za kayi gidan aure ta Nazee ya mik'e tsaye yace ni banida lokacin cigaba da sauraro wannan surutu naki na fita amma fa anjima zan dawo ki ajiye min fura kaka ta bishi da harara. Raheela na shiga d'aki tafad'a bisa gado tafashe da matsanaci kuka shikenan yanzu naci amana yaya na'eema na kuma k'arya alk'awali da na d'aukar mata, oh ni raheela naga takaina zan aure ```MIJIN 'YAR UWA TAA ``` amma kuma sun ce addini bai hana ba to amma ```ana bari Halak don kunya ``` da sauri ta d'auko wayarta ta kira ayshat ta zaiyane mata abunda ke faruwa tun kafin ta dasa aya Ayshat ta kurma ihu da sauri raheela ta cire wayar daga kunne ta wannan banza tanaso tafasa mini dodo kunne mtss ta jefarda waya tacigaba da shshekar kuka. Amar yana fita gidan sa yanufa zuciyarsa cike da tsan-tsa farin ciki marar misaltuwa yad'aga hannu sama yace _Allah na gode maka da kanufi ni da samu farin ciki na Allah ka k'arawa Annabi Wasila da fadila_ Mutum na farko da yafara kira shine Dr kabeer ya sanarda shi abin farin ciki da yasame shi cikin tsanani jin dad'i Dr kabeer yace _congrats_ aboki na burin ka yacika nasamu taurarowa ka ina tayaka murna Allah yabaku zama lafiya ya kad'e fitina a tsakani ku. _Ameen kb na gode da wannan addu'a_ suna gama waya Dr kabeer ya dinga turawa _friends_ d'in su _text_ na d'auri aure. Umma hajara na zaune a falonta tana waya da aunty asabe na Shiga uku aunty asabe watan kunya ta yatsaya Amar zai aure shegiya yarinya nan da tsana da bana fatar na cigaba da bude ido ina ganita. Shikenan kashi ki yabushe hajara mafita d'aya ta rage miki ki tashi tsaye ki shiga ki fita ki hanawa raheela zaman lafiya a gidan Amar. Wallahi ashirye nake aunty asabe ko zan rasa rai na sai na tarwatsa rayuwa raheela Rai kuma hajara, me kuma ya kawo zance rasa rai"? Ranar biyan bukata aunty asabe rai ba'a bakin komai yake ba a yadda nakeji zuciya ta in har buk'ata ta za ta biya komai zan iya aikatawa. Ke fa sokuwa ce hajara in kin rasa ranki ubanwa zai cigaba daga inda ki ka tsaye"? Ki budewa kunne ki da kyau saurare ni ki shirye akwai wani hatsabibin boka a gari _Enugu_ aikin sa na matukar tasiri, shikenan aunty asabe ki shirya rana assabar mu kai masa ziyara. ```WASHE GARI ``` Tun da misali k'arfe _9:00am_ yaya hafsat tad'auki raheela suka tafi gidanta inda Hajiya Zaituna mai gyara amare tafara gyara raheela da misali k'arfe 11:09am Ayshat da zainab da wasu daga cikin 'kawaye raheela da zainab ta gaiyato suka fara cika gidan yaya hafsat kallo d'aya za ka yiwa amarya kagano bata farin ciki da wannan aure. Da misali k'arfe _2:30pm_ aka d'aura aure ```Amar Muhammad matawalle da Raheela Abdullah matawalle ``` a bisa sadaki naira dubu _hamsi_ lakadan ba ajalan ba yayida ango Amar yasha farar shadda d'iki babbar Riga kansa d'auke da bak'ar hula kunbe sai faman gaisawa da mutane yake yi kana kallon fuskarsa za ka hango tsan-tsa farin ciki da yake tartare da shi.... Jeeddah Aliyu🌹 [04/08 7:19 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [04/08 1:20 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 8⃣5⃣ Da misali k'arfe _4:30pm_ akayi kamu raheela tayi matukar kyau, Ayshat da zainab sai faman tsokana ta sukeyi bayan antashi daga kamu ne bahijja matar Nazee ta rik'o hannu raheela tace zo mu je yayanki naso ganin ki Nazee na zaune a cikin motarsa bahijja tak'araso da raheela ta d'an kwakwasa _glass_ d'in mota had'e da cewa _honey_ kafito ga ta na kawo ma Nazee yafito daga cikin mota fuskarsa d'auke da tsantsan farin ciki yace _congratulation my sister_ ina taya ki murna ganin wannan rana mai d'ibin albarka Allah yabaku zaman lafiya da ha'kuri zama da juna wallahi raheela yau ina cikin tsanani farin ciki marar misaltuwa, na gani wannan rana da burin yaa Amar yacika na mallaka ki a matsayin matar aure sa tun daga ranarda na fahimce cewa yaa Amar yana sonki nake addu'a Allah ubangiji ya mallaka masa ke sai gashi yau Allah{s.w.t} ya nuna mini wannan rana ina rok'oki raheela ki taimaka ki bude k'ofar zuciyarki ki samawa yaa Amar fili wallahi _guy_ nan yana matukar sonki fiye da tunani ki. A hankali tad'ago idanu ta da ke tsiyaya hawaye tana kallo Nazee daga bisani tace dama yaya Nazee baka tare da ni kai ma kana farin ciki da auren ```MIJIN 'YAR UWA TAA ``` da nayi"? Duk wani masoyi ki raheela zai yi farin ciki da aure ki da yaa Amar ni dai rok'o na gareki ki kwantarda hankali ki shi ```SO``` a hankali yake Shiga zuciyar dan Adam a sannu za ki waye gari ciki soyayya yaa Amar kinsan _guy_ bashida sauki a fagge soyayya haka yake kamar _Romeo_ Raheela batasan lokacin da murmushi ya kunbuce mata ba yayida Nazee da matarsa bahijja suka kyakyale da dariya, bahijja tace ko ke fa matar likita wannan murmushi da ki kayi baki ga yadda yayi masifar yi miki kyau, raheela ta galla mata harara tace ke ma kina goyon bayan mijinki koh"? Nazee yace a wannan tafiya raheela babu mai goyon bayanki, ina zuwa bari na d'auko miki _special gift_ d'in da na kawo miki ya bude mota yafito da wani abu yana lullube da _raping paper_ ya mik'awa raheela cikin sanyi jiki raheela ta karb'a tace na gode yaya Nazee. Bahijja tace to kawo na tayaki d'auka wannan abi daga sa sai yayi nauyi kinsan ba'aso amarya tana wahala. Da dare za'a gabatarda _Dinner party_ Raheela da 'kawaye ta zaune a _bedroom_ d'in da aka ware musu a gidan yaya hafsat kowace su tasha _makeover_ raheela sai bin su da kallo takeyi daga bisani tace in tambaye Ku mana"? Zainab ta ajiye turare da ke riK'e a hannuta bisa _dressing mirror_ ta zauna kusa da raheela tace miye tambayanki matar likita"? Mtss...raheela taja tsoki tace na tsani wannan sabon sunan da ku ka lak'a min ya akayi naga kusan kaya iri d'aya da alama anko ne"? Kwarai kuwa anko ne yaya hafsat ce ta raba mana shi a kyauta. Raheela ta yatsine fuska tace hmm wahala ce bata 'kare mata ba shiyasa har take raba anko kyauta zainab ta tabe baki had'e da cewa amarya bakya laifi ko kin kashe d'a masu gida raheela tak'ara harzu'ka sai cika take tana batsawa zainab tajuya tacigaba da sabga gabanta, raheela ta mik'e tanufi _gift_ d'in da yaya Nazee yabata ta yaye _raping paper_ tangameme photo su da yaa Amar ya baiyana raheela ta zaro ido sakamako gani ta tsaye a gaban yaa Amar shi kuma yadaura yatsa sa akan _lips_ d'inta tsawon rayuwa ta bata tab'a sani tayi photo da yaa Amar ba gari yaya Nazee yasame wannan _photo_? Ciki zumudi Ayshat tak'aso wurin raheela tace _wow perfect couple_ wallahi raheela kunyi masifar kyau yaushe ku kayi wannan _pic_ d'in"? Bansaniba raheela tafad'a kaitsaye had'e da ture Ayshat tanufi 'kofar fita taci karo da yaya hafsat cikin bacin rai yaya hafsat tace wannan wane irin iskanci ne raheela ya za'ayi ki bar aunty zaitun zaune tana jira ki"? Raheela tayi rau- rau da idanu tace kiyi ha'kuri yaya hafsat, fitowa nan da nayi chan na nufa. Aunty zaitun ta baje kwarewa had'e da bajinta ta hanyar tsantsarawa amarya raheela _make-up_ yaya hafsat tashigo hannuta d'auke da k'aton kwali tafito da _wedding gown_ blue & golden colour ta mik'awa raheela cikin sanyi jiki raheela ta karb'i _gown_ d'in tasaka yayida aunty zaitun ta nad'a mata _Golden head_ tubarakallah masha Allah raheela tayi matukar kyau tafito amarya sak Yaya hafsat ta rik'o hannu raheela suka nufi farfajiya gidan tuni an kwashe 'kawaye raheela zuwa _hotel_ d'in da za'ayi _Dinner_ wata ba'kar mota kirar _Hummer Jeep_ tasha _Decoration_ da _Balloons_ yaya hafsat tanufa da raheela ta bude 'kofar ta umurce raheela da tashiga babu musu balle gardama raheela ta kutsa kai tashiga motar saboda zuwa yanzu ta sadakat domin bakin al'kalami yabushe ta zama, mallakin yaa Amar tana dusana duwawu ta bisa kujera k'amshi turare sa na _Pure blue_ yad'aki hanci ta, da sauri tajuya kusa da ita yana zaune yasha dakakiya shadda _blue colour_ sai faman danna wayarsa yakeyi raheela tasaki ajiyar zuciya yayida _driver_ yaja mota suka d'auki hanya tafiya kurame sukayi ba Wanda yatankawa d'an uwansa.... [04/08 7:18 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 8⃣6⃣ Raheela ta sada kanta k'asa tana wasa da zobe yatsa ta kamar daga sama taji sautin murya sa _you look so beautiful & gorgeous my lovely wife_ A tsoroce raheela tadago ga mamaki ta saida taga kamar bashi bane yayi magana domin yadu'kufa wurin danna wayarsa kuma babu wata alama da ke nuna mata shi d'in ne yayi magana don haka tak'ara sunkuyarda kanta, har suka isa _hotel_ d'in kanta na 'kasa jin karar bude k'ofa yasa tadago _driver_ ne ya bude mata k'ofa yace ranki shidad'e mu iso a hankali ta sauke 'kafafu ta waje tasoma tafiya Amar yak'arasa kusa da ita batare da yace da ita komai ba ya rik'o hannuta, a sanyaye ta juya ta kalle shi yayida shi kuma gabanta sa kawai yake kallo suna k'arasa 'kofar da zata sada su da _Hall_ 'kawaye raheela tare da _friend's_ d'in Amar suka Mara musu baya abin gwanin ban sha'awa suna shiga _Hall_ d'in gaba d'aya mutane da ke ciki suka mik'e tsaye domin girmamawa ga ango da amarya yayida _Dj bad boy_ yasaki _slow music_ mai ratsa zuciya a hankali ango da amarya suke tafiya akan lausashe _blue carpet_ tamkar masu tausayi taka 'kasa saida suka zauna a _high table_ sannan mutane suka zauna tsawon dak'i'ka biyar zuwa shidda _Dj bad boy_ yad'auka yana kawata _Hall_ d'in da _cool music_ daga bisani ```MC``` ya d'auki _microphone_yakira Dr kabeer yabada tarihi ango don tsabar iya yi na Dr kabeer har da fad'ar yadda Dr Amar yake tsanani so raheela yana dasa aya! Gaba d'aya _Hall_ d'in aka d'auki tafi raf-raf ```MC``` baiyi 'kasa da guiwa ba yak'ara za'kula babbar 'kawar amarya zainab tabada tarihi raheela ashe ba Dr kabeer kadai ya iya wuce wuri ba ko zainab kwarariya ce domin yadda ta tsaro tarihi soyayya Amar da raheela sai ka rantsi da Allah hakan yafaru da gaske tana mik'awa ```MC``` _microphone_ aka d'auki tafi da sowa. Raheela taja d'an k'aramin tsoki Amar ya kalle ta ya galla mata harara da sauri ta d'auke fuskarta, yayida shaharare mawaki nan da duniya ke yayi sa wato ```Nura m Inuwa ``` yasoma wak'e ango da amarya cikin zazzak'a muryar sa tuni fili yakachame sai watsi ake masa da Naira daga bisani ```MC``` ya gaiyato ango da amarya domin suma su fito su chashe Amar yarik'o hannu raheela suka fito a tsakiya fili sai lik'i ake musu sai misali k'arfe _12:30_ na dare aka watsi, Amar yana rik'e da hannu raheela suka nufi mota raheela ji take kamar ta kurma ihu suna isa gida _driver_ yayi parking suka fito gidan yayi tsit kamar babu mutane a ciki har raheela ta juya tanufi _part_ d'in kaka chan 'kasan ma'koshi Amar ya Kira ta raheelaah ya ja sunanta kafin ta amsa sai ya juyo da sauri ya zo gabanta ya 'kura mata idanu 'kasa juri kallo da akeyi mata ta sada kai 'kasa ba zato balle tsanmani yafisgo ta da k'arfi tafad'o k'arji sa ya rungume ta tsam-tsam a jikinshi, gaba raheela sai faman duka tara-tara yakeyi jikinta na kyarma amma ta kasa Kwacewa, jin tayi yana shafar ta sai tafara 'ko'kari zamewa _head_ d'in kanta ya fad'i jela gashi kanta ya sauka bisa kafad'unta jin takeyi tamkar an jona ta a lantarki haka take ji" Cikin sanyi murya yake magana "Raheelaaah miyasa akoda yaushe ki ke so ki musgunawa zuciyata"? Da kinsan yadda nake sonki da kin tausaya mini kinbani masauki komai 'kan'kanta shi a zuciyarki Dan Allah raheela ki tausaya min ki so ni, raheela ta girgiza kai hawaye na zuba daga idanu ta tace ba laifi na bane yaa Amar laifi zuciya ta ne da takasa amincewa da kai a matsayin masoyi, Amar yadago fuskata ta runtsi idanu ta Amar tsura ma _pink lips_ d'inta idanu a hankali ya had'e baki shi da nata yasoma tsotsan saida yagaji don kanshi yasaketa, raheela tafara ja da baya daga bisani ta ruga da gudu tashiga _part_ d'in kaka Amar ya bita da kallo yayida shauk'i sonta yake ratsa sassa jikinsa yaduk'a yad'auki _head_ d'inta yashige tsoho d'aki sa. ```WASHE GARI ``` A kayi walima bayan an kamalla walima aka soma shirye-shirye tafiya kai amarya _Abuja_ raheela na zaune a falon kaka iyayye ta suka saka ta gaba suna mata nasiha, tsawon lokacin suka d'auka suna mata nasiha raheela sai faman kuka takeyi gani yadda raheela take kuka tayi matukar ba kaka tausayi, kaka takasa juri jin kuka ta ta tashi tashige d'aki daddy yad'auko _key_ d'in tsadadiya mota ya ba raheela Abba ya mik'e yad'ago ta ya rik'o hannu ta yanufi waje da ita yasakata cikin sabuwar mota ta wata tsohuwa 'yar uwa su daddy ta zauna kusa da raheela zainab ta zauna a _seat_ d'in gaba _driver_ yaja mota yayida saura mutane 'yan rakiya amarya suka shiga motoci aka d'auki hanyar _Abuja_ ........ Jeeddah Aliyu🌹 [07/08 8:28 am] Jeeddah Aliyu🌹: [06/08 8:58 am] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 8⃣7⃣ Tun lokacin da suka d'auki hanyar _Abuja_ raheela take ta faman kuka tun 'yar Tsohuwa da zainab suna bata hak'uri har suka gaji suka zuba mata ido, tsanani kuka da takeyi ya haddasa mata ciwo kai had'e da zazzabi mai zafin gaske koda suka shiga garin _Abuja_ raheela batasan Inda kanta yake ba saboda har jiri takeji kaitsaye gidan Amar aka dosa da ita raheela nagani sun shiga _gate_ d'in gidan tasake rushewa da kuka _driver_ yayi parking tsohuwa ta rik'o hannu raheela suka shiga cikin gida, da sauri raheela ta runtsi idanu ta har aka shigarda ita cikin _bedroom_ d'in ta idanu ta na rufe a wannan karo zainab ce ta zaunarda ita a gefen gado, duk da haka idanu ta na nan rufe Ayshat ce tashigo d'aki tace jama'a lokacin sallah magarib yayi don haka duk Wanda yasa yana sallah yatashi yasauke farali tuni mutane da ke cikin d'akin sun fice d'akin yayi saura daga Ayshat sai zainab suka saka raheela a tsakiya suka soma yi mata nasiha had'e da lallashi Ayshat tace Dan Allah _besty_ ki danne zuciyarki kiyi 'ko'kari ki kyautatawa mijinki a yanzu zance kina sonshi ko bakyaso yak'are zama ne zakuyi na har abada karki bari shedan ya yi tasiri akanki yahana miki Neman aljana ki domin gidan Amar anan ne za ki sami aljana zainab ta karb'e zance ta hanyar cewa wallahi raheela kinyi dace nasamu mijin irin yaa Amar wani abin sha'awa yadda yake tsanani sonki don haka ina baki shawara da kiyi watsi da duk wani fitsara da rashin kunya da ki ke yi masa saboda a yanzu yana matsayi mijinki na sunnah Kisani duk wani mumuna abu da ki ka furta akan sa zunubi za'a rubuta miki in har ada kina masa kallo na yayanki ko kuma ```MIJIN 'YAR UWA KI ``` a yanzu ya tashi daga wadannan matsayin ya haura a babban matsayi na kasance wa abokin rayuwarki da kyar raheela d'ago idanu ta da sukayi masifar yi mata nauyi sakamako ciwon kai da yake barazana tsaga kanta gida biyu, tasoma kallo Ayshat da zainab daga bisani ta sada kai kasa tana sharar hawaye da gefen mayafinta tarasa wance kalma za tayi amfani da ita domin su fahimce ta Ayshat tayi 'kasa da murya tace _please besty_ karki wargazawa Dr Amar _budget_ ki bashi had'i kai Ku raya _first night_ d'inku cikin so da 'kauna ina tabbatar miki gari na wayewa za ki ji ki tsunda a cikin soyayya mai zafin gaske. Mtsss raheela taja dogon tsoki had'e da mik'ewa tashiga _bathroom_ Ayshat da Zainab suka kyakyale da dariya har suna tafawa, k'arfe _9:30pm_ aka debi mutane zuwa gidan yaya hafsat achan za su kwana washe gari su koma _Kaduna_ yayida Ayshat ta tafi da Zainab gidanta aka bar raheela ita kadai a _bedroom_ tana Sana'a ta, ta kuka musanman yanzu zazzabi ya'kara tasiri a jikinta saboda yadda take rawa sanyi har ha'kora ta ke had'ewa, da misali 'karfe _10:9pm_ Dr Amar yadanno hanci motarsa a farfajiya gidansa yayi _parking_ yafito yasha shadda _marrow colour_ tayi matukar yi masa kyau cikin natsuwa yake tafiya yana Shiga falon yaji tsit kamar babu mai rai a cikin gidan yanufi _bedroom_ d'inshi da ke _upstairs_ ya kalle d'akin raheela yasaki ajiyar zuciya, yawuce yashiga nasa wanka yayi yasaka _pajamas_ yafeshe jikinsa da turare har yayi niya ya kwanta sai kuma yafasa Ya bude 'kofa yafita d'akin raheela yanufa duk da bashida tabbaci d'aki yana bude ya murd'a _handle_ ga mamaki sa sai yaga 'kofa ta bude kaitsaye yanna kai ciki had'e da yi sallama, shashekar kukanta ne ya amsa masa sallama, tana kwance a tukure wuri d'aya sai faman rawa sanyi takeyi had'e da rera kuka da sauri Amar yanufi wurinta _subhanalillah_ wai har yanzu raheela baki daina wannan kuka ba"? Yad'ago ta yaji jikinta yayi zafi rau yak'ara rudewa ya manna ta a jikinshi ta aza kai a k'irjinshi tana ta zurarar da hawaye. Ya sunkuyo setin kunnenta yayin da ya fitarda wani huci Mai d'umi a kunnenta ya lumshe ido ya shak'i 'kamshin turare jikinta, yayi magana cikin wata lallausar murya mai laushi da gard'i gaske. Raheela, kukan me kike yi ne"? Me nayi miki da ki ka tsane ni"? Me nake yi miki wanda yake baki haushi har yake haddasa miki 'kiyayya ta in daina"? Me kike so a duniya raheela in ba ki ko zuciyarki za ta so ni"? Me kike 'ki a duniya in daina yi miki ni dai fatana ki so ni raheela"? Idan hawaye ki yana zuba ji nake kamar an zuba min dalmar wuta a cikin zuciyata. Hankalina yana fin naki tashi muddin kika tayarda hankalinki raheela ke rayuwata ce bugun zuciyata, farin ciki na dole nayi tattalinki had'e da yak'i Neman za6e kujera zuciyarki ke amana ce a gareni tamkar an bani ajiyar kwai cikin cokali haka nake ji a hannuna. Farin ciki na naganki cikin walwala da nishad'i kifada min raheela me kike so a duniya duk wuya duk runtsi zan nemo miki shi ko da kuwa zan rasa raina muradina ki amince ki bani masauki a zuciyarki. Raheela ta d'ago a hankali ta dube shi yayi da ta ga hawaye ya cika masa ido ta mayar da kanta bisa k'arjinsa cikin shashekar kuka kamar za ta shed'e saboda kukan yaci k'arfinta ga kuma zafin zazzabi tace kayi han'kuri yaa Amar ba laifi na bane laifi zuciyata ne da tak'asa amincewa ta so ```MIJIN 'YAR UWA TAA ``` Amar yayi shiru yayin da zuciyarsa take tafarfasa da zafin son raheela a hankali ya zareta daga jikinsa ya shiga _bathroom_ yafito da d'an k'aramin _bucket had'e da _towel_ Ya tashe ta zaune ya ye mayafin jikinta ajiye a gefen gado ya zuge _zip_ d'in rigarta da sauri ta rik'e masa hannu tayi rau- rau da idanu tadawo kallar tausayi Amar ya yi murmushi kumatu sa suka lotsa{dimple} yace jikinki ya yi zafi sosai kina da bu'katar taimako na ya ture hannuta yak'arasa zuge _zip_ d'in da sauri ta runtsi idanu ta sakamako balle _bra_ d'inta da ya yi..... [07/08 8:27 am] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 8⃣8⃣ Ya tsoma _towel_ d'in cikin ruwa masu d'an d'umi-d'umi yasoma goge mata jiki har yagangaro kan 'kirjinta anan kan Amar kasa _control_ d'in kansa Ya yi, _yajefar da towel_ yafara ya motsa ta sai wani masifafe numfashi yake sauke wa ya lala6o bakinta ya had'e da nasa yana tsotsa yayin da raheela ta ke kuka 'kasa-'kasa ya rad'a mata ba abunda zan yi miki raheela kidaina kuka, sai da yarage zafi sannan ya d'aura ta a k'irjinshi ya rungume ta yana jin yadda zuciyar ta take bugawa da sauri da sauri ya shinfid'e ta yafita tana gani yafita ta tashi da sauri ta mayar da rigarta yashigo hannu shi rik'e da _tea cup_ ya mik'a mata babu musu ta k'ar6a tasoma kurba a hankali Amar yayi tsaye yana kallonta saida ta shanye _tea_ d'in tass sannan ta mik'a masa _cup_ ya had'e hannuta da cup yarik'e ta sunkuyarda kai 'kasa, _raheelaah_ ya kira sunanta shiru bata amsa ba yashafi goshinta yaji tafara zufa yace sauki yasamu tun da har kinfara zufa za kiyi wanka na had'a miki ruwa"? Cikin sanyi murya tace _Na gode_ kayi tafiyarka kawai tana k'arasa fadar haka tayi kwaciyar ta har da su rufa da _blanket_ ya yi tsaye sororo yana kallonta ya kad'a kai ya kunna mata Ac {Air condition's} yafice daga d'aki tana gani yafita tasauko ta datsi 'kofarta da _key_ ta haye gado zuciyarta cike da alhini irin zaman da za tayi da yaa Amar take tafara sak'e-sak'e yaa Amar yana matukar sona in na kwantarda hankalina wata rana zan waye garin cikin sonshi Amma kuma in hakan ta kasance na tafka abin kunya domin na son ```MIJIN 'YAR UWA TAA ``` kuma na k'arya alk'awali da na d'aukawa yaya _na'eema_ har abada ba zan yi sake da _so_ yaa Amar zai Shiga zuciyata, to miyasa duk lokacin da yaa Amar yarab'eni nakeji sabon al'amari yana ziyarta ta me hakan yake nufi"? Mtss bai kamata na dinga wahalar da kwakwalwa ta wurin neman amsa tambayar da batada amfani a wurina da wannan gurguwa shawara bacci ya yi nasara kwashe raheela. Amar yana shiga _bedroom_ yafad'a kan gado sa yasauke gwaron numfashi yasoma tunani lallausar fatar raheela da 'kirjinta masu tsanani laushi da tsantsi uwa uba sanyaye 'kamshi turare ta da ya yi nasara k'ara tayar masa da sha'awa ya lumshe _sexy eye's_ d'insa masu cike da tsanani bukatar Raheela, da kyar ya mik'e yanufi _bathroom_ yasake wanka had'e da alwala yasanya farar jallabiya ya shinfid'a _pray mat_ yafara zuba nafilla. ```WASHE GARI ``` Sai misali k'arfe _8:00am_ raheela ta falka a gurguje tafad'a _bathroom_ tayi wanka da alwala bayan ta gabatar da sallah sai lokacin tasamu tak'are wa _bedroom_ d'inta kallo a tunani ta kayan d'aki na'eema ne sai yanzu ta fahimce duk abunda ke d'akin sabon ne tasauke ajiyar zuciya, ta zauna gaban _dressing mirror_ tayi _simple make-up_ duk da tayi matukar rama hakan bai hanawa kyau ta baiyana ba wani dakakke _lace_ orange colour tasaka ya yi matukar kar6a fata ta wuyanta da kunneta sun sha _whites gold_ sai faman zabga 'Kamshi takeyi ta nufi _parlour_ ....... Jeeddah Aliyu🌹 [07/08 2:48 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [07/08 11:33 am] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 8⃣9⃣ Tayi tsaye tsakiyar _parlour_ tana kallo yadda aka chanza masa tsari sai kace ba _parlour_ yaya na'eema ba wasu zafafa hawaye suka zubo mata tasaka bayan hannuta ta goge tacigaba da zagaya gidan duk wani abu da na'eema ta yi rayuwa da shi an sauya shi ko tsinke babu na yaya na'eema a gidan _Allah sarki duniya shikenan an shafe babi yaya na'eema a duniya_ daga karshe tashiga _kitchen_ tana kallon tsari da akayi mata hatta cokali {spoons} d'in da ke cikin _kitchen_ d'in _lemon green_ ne motsi taji a bayanta juyawar da za tayi ta had'a ido da lamtana{idan mai karatu bai mata ba lamtana itace mai aikin mami} ta zaro idanu had'e da kurma ihu lamtana daga sama kika fad'o ne"? Lamtana ta kyakyale da dariya tace ae tun jiya nake gidanan likita bai fad'a miki tare muka zo ba"? Raheela ta tabe baki tace watakila ya manta ne, lamtana tace da kyar mami ta amince na dawo nan da zama cikin tsanani jin dad'i raheela ta rungume lamtana tace kai amma kuwa naji dad'i ko ba komai nasami abokiyar fira, lamtana ta washe hak'ora tace nafiki farin ciki uwar d'akina shiyasa na tashi tun asuba na had'a mu Ku _breakfast_ raheela ta kyakyale da dariya tace bakida dama lamtana Hmm uward'akina irin wannan gida da likita ya k'era miki ni bantaba gani irin sa ba wannan shi ake Kira da ```Aljanna Duniya``` dank'ari masu abu da abin su 'yar garuwa ta ga hadari tace bari mu zubarda namu ae kuwa raheela tak'ara kyakyalewa da dariya kamar daga sama taji murya sa yana fad'ar duniya tayi miki dad'i raheela irin wannan dariya wane irin labari ne lamtana take ba ki da ya sanya ki nishadi"? Tuni nishadi da ke fuskar raheela yabace fat tayi wani murtuk'e fuska kamar ba ita bace take dariya, Amar ya yi tsaye hannu sa na dama yana cikin aljihu wando material _black colour_ material d'in irin mai tsanani taushi nan ne ga shi kuma raga- raga har ana hango _White vest_ d'insa kayan sunyi masifar kar6a jikinsa abu ga farar fata cikin bak'i kaya karo na farko da raheela ta tsurawa Amar ido nan take tagano tsan-tsan kama da sukeyi sai yau ta yarda da ake cewa tana kama da Amar kasa d'auke idanu ta tayi akan shi saboda ba k'aramin kyau ya yi mata ba yayin da shima Amar yakafe ta da nasa idanu gani yanayi kallon da suke yiwa junan su yasa lamtana taji kunya yakamata da sauri tafice daga _kitchen_ d'in cikin tafiyar 'kasaita ya tunk'aro ta a hankali take ja da baya bata ankara ba taji tayi karo da _kitchen cabinet_ dole taja tayi tsaye ta kuma sada kai k'asa ya k'araso daf da ita ya zura hannu shi ta bayanta yadafa _cabinet_ ya yi mata rumfa da k'irjinsa ta yadda ba za ta iya tsarewa ba yasaka hannu sa d'aya yad'ago fuskarta da sauri ta runtsi idanu ta ya busa mata iska bakinsa akan fuskarta tasaki ajiyar zuciya mai k'arfi Amar yak'ara matsita k'irjinsa yana gugar nata, chan 'kasan mak'oshi yakira sunanta _raheelaah_ wani irin masifafe _shock_ ya ja ta ji takeyi kamar ana jaye jini jikinta tak'ara lumshe idanu ta yacigaba da kiran sunanta _raheelaah_ cikin rawar murya ta amsa _Na..'am_ Ina neman wani d'an k'aramin taimako a wurin ki ina fatar za ki taimaka min"? Raheela da tuni tafara tsorata da lamari yaa Amar tace Allah yasa zan iya Da sauri yace za ki iya raheela za ki iya Shikenan menene taimako naka"? _please_ raheela kada kice a'a domin rashin taimaka min zai iya jefa ni cikin wani mayuwaci hali. Ni fa nafara gajiya da tsayuwa kafad'i buk'atar ka in zan iya na taimaka maka in kuma ba zan iya ba sai ka nema a wani wuri _No raheelaah stop saying dat_ iya taimako ki nakeso _please baby I need your help_ Na ji zan taimaka maka d'in" Amar ya yi murmushi yace _promise_?? Cikin yanayi na gajiya raheela tace _Yes yaa Amar I promise you I Will help you_ _Raheelaah_ Yaa Amar kafad'i magana ka saboda nagaji da wannan kiran sunan nawa da ka ke yi _Raheelaah so nake ki taimake ni ki ceto numfashi na ki amince na tsotsi Jan baki ki_ Raheela batasan lokacin da tafara kalma shahada ba tace akan Jan baki ne tun d'azu ka ke bata min lokacin"? Amar ya girgiza kai yadawo kala tausayi ya yi 'kasa da murya yace shine raheela ina tsanani son Jan baki nan in har ban tsotsi shi ba komai zai iya faru da ni kuma kinyi min alk'awali za ki bani Raheela tasaki ajiyar zuciya daga bisani tace kai kuwa yaa Amar me za ka ji a cikin _Jan baki_ ?? Sinadari da yake cikin sa nakeda buk'ata kin amince na tsotsi raheela"? Raheela ta bata fuska ji takeyi kamar tafashe da kuka sai dai batada yadda za tayi dole ta amince da buk'atar yaa Amar ta huta da jarraba sa Ta yatsine fuska tace _okay_ ka tsotsi amma ina so kasani wannan shine na farko kuma na k'arshe ko za ka mutu bazan 'kara amincewa ka tsotsa mini _lips_ Cikin tsanani jin dad'i Amar yace haba Baby naa ni da ke mutu karaba ne ko kin tab'a gani inda aka raba anta da jini"? Ka ga malam ni wannan bai shafeni ba kayi abunda yake gaban ka saboda ni yunwa nakeji Amar yace to ki bani mana, cikin bacin rai raheela ta turo masa bakinta, yasaki murmushi jin dad'i yasaka halshe sa yana lasar _lips_ d'inta daga bisani ya had'e bakin sa da nata yadinga tsotsa jikin raheela yafara rawa tasoma k'ok'ari kwantar kanta ta tattaro dukan k'arfinta ta ture shi saidai kamar ta ture giwa saboda ko motsi Amar bai yi ba gani haka yasa ta sulala 'kasa shima bita ya yi ya zauna a gabanta yayin da hawaye suka wanke mata fuska yasaka halshe sa yana lasar hawaye ta gaba d'aya Amar ya dagulawa raheela lissafi takasa gano wace duniya take ciki, jin tayi ya mik'arda ita tsaye mu je ki ci abinci kinji baby naa? Raheela kan tadawo kamar ragumi da akala sai yadda Amar yaga dama ita ya ja hannuta suka fice daga _kitchen_ kaitsaye _darning area_ yanufa da ita ya ja kujera ya zaunarda ita ya bude _Warmer's_ ya yi mata _serving_ din _chips_ had'e da _source_ d'in kwai da anta yaji _carrot_ da _cabbage_ sai 'kamshin _spices_ ke tashi ya tura mata _plate_ gabanta ya zuba kunu gyad'a a cup ya ajiye mata, yace _bissimillah_ da yake raheela naji shegiyar yunwa bata 'ki tayi da Amar yayi mata ba.... [07/08 2:44 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 9⃣0⃣ A hankali take cin _chips_ d'inta tana 'korawa da kunu gyad'a goga naku ya tsura mata ido, duk lokacin da tad'ago sai sun had'a ido yasa ke mata lallausan murmushi a zuciyarta tace _crazy man_ batasan cewa magana da tayi yafito fili ba sai jin tayi yace _yes baby I'm crazy about you_ Raheela ta zaro idanu had'e da cewa Yakamata ka yiwa kanka fad'a _Co's me I don't have time to do dis useless things_ Amar ya yi murmushi yace _baby you make a mistake_love is not a useless love is most precious gift from God life without love is brutality_ Mtss.. Raheela taja tsoki da k'arfi ta dire _fork_ d'in hannuta cikin _plate_ ta mik'e cikin zafin rai da sauri Amar ya rik'o hannuta yace _I love you raheela your love make me crazy your love is the most precious gift I have never had You are highly treasured so give me a chance to show how much I love you_ Ka sake mini hannu ina rok'o ka da kadaina Shiga sabga ta _Co's I don't love you any more & I will never let's my heart to love you_ A sanyaye yasaki hannuta da gudu ta haura sama tashiga d'akinta ta fad'a kan gado tafashe da kuka tace _I'm sorry yaa Amar I don't means to hurt your feelings_ duk abunda nakeyi ina shi ne saboda kai ```Mijin 'yar uwa taa``` ne banaso na k'arya alqawali da na d'aukawa yaya na'eema jin ana _knock_ d'in kofa yasa ta tashi da sauri ta nufi _dressing mirror_ ta goga _powder_ ta zizzara kwali a idanu ta har ta d'auko Jan baki za ta Shafa taji an 'kara yi _knocking_ ta ajiye Jan baki tanufi 'kofa ta bude zainab da Ayshat ta gani tsaye suna dariya tabe baki tace miye haka da za Ku dinga yi mini _knocking_ sai kace gidan bak'o Ku ne"? Suka 'kara kyakyalewa da dariya har suna tafawa abunda ya harzuk'a raheela kenan tace _okay_ na fahimce abin naku iskanci ne sai Ku yi Ayshat tace Allah ya huci zuciyarki matar likita kinada _guest_ a parlour raheela ta yatsine fuska ta ra6a gefen su ta wuce da sauri zainab tace haba raheela wannan wace irin kwaliya ce"? Ras gaban raheela yafad'i cikin sark'ewa halshe tace me...kika..gani ne"? Zainab tayi murmushi tace kawai gani nayi kin Shafa kwali kinyi jagira amma baki Shafa Jan baki ba raheela ta galla mata harara had'e da cewa banyi ra'ayi shafawa ba ko za ki sani dole ne"? Karaf Ayshat ta k'arbe zance ta hanyar cewa banda abinki raheela ya za'ayi kiyi kwaliya ba Jan baki Tsanani bacin rai yak'ara lullube raheela domin ta tsani kalma Jan baki ga kuma wadanan 'yan jarida suna so su k'ure mata maleji a hassale tace na Shafa yaa Amar ne ya tsotsi shi yanzu Sai hankali Ku ya kwanta tun da nafad'a mu Ku tana 'karasa magana tanufi _parlour_ k'asa zainab da Ayshat su ka kalli juna had'e da tintsirewa da dariya, raheela na shiga _parlour_ ta gaisa da 'yan uwa su na Kaduna Wanda suka kwana a gidan yaya hafsat daga nan sukayi mata sallama za su juya Kaduna yaya hafsat taraba masu katuwa jakka mai d'auke da photo Amar da raheela jakka cike take da kaya raheela ta rungume zainab tace shikenan zee za ki tafi ki barni koh"? Zainab tace aure kenan raheela dama yagaji haka Allah yabaku zaman lafiya yabaku zuri'a tagari raheela tana kallo zainab tashiga mota _driver_ yaja suka tafi ita da Ayshat da kuma Yaya hafsat suka juya cikin gida...... Jeeddah Aliyu🌹 [07/08 7:47 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [07/08 5:45 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 9⃣1⃣ Nasiha yaya hafsat da Ayshat suka cigaba da yi mata sai misali 'karfe _8:00pm_ na dare suka wuce, raheela batayi wani damuwa ba saboda tana tare da lamtana bayan tadawo daga rakiya su ta wuce _bathroom_ tayi wanka ta bude _wardrobe_ gefen da _sleeping dress_ d'inta suke ta d'auko wata 'ya yaloluwa rigar bacci _light pink colour_ tasaka tashafe jikinta da humra had'e da turare _explore_ ta d'auki _lollipop_ ta 6are ta jefa baki tana tsotsa tad'auki phone d'inta saboda kusan _3 day's_ kenan batada caji tafice daga d'akin ta nufi _parlour_ 'kasa lamtana na zaune ta 'kurawa akwati talabiji ido ya gani yadda tasha gala yasa raheela ta lab'a6o ta bayanta tace kee! A tsorace lamtana tace _wayyo Allah_ Raheela ta kyakyale da dariya tace yaushe za ki daina wannan tsoro naki lamtana"? Lamtana tace babu rana saboda matukar ina tare da ke ba za ki daina tsorata ni ba Raheela ta zauna bisa _two star_ tana murmushi tace lamtana d'an saka mini phone ina a caji suna kallo lamtana na bata labari Amar ya yi sallama yashigo _parlour_ lamtana ce ta amsa masa sallama tace barka da zuwa likita" Amar ya zauna kusa da raheela yace yauwa lamtana ya juya wurin raheela ya ga ta murtuk'e fuska ya dungure mata kai yace ke wannan shan Omo fa"? Lamtana ta mik'e tanufi d'akin da aka ware mata, raheela ta galla masa harara ya yi murmushi yace laifi me nayi kuma ake harara na"? Mtss.. Ta ja tsoki a rayuwa ta bantaba gani _heartless_ irin ka ba yakamata ace zuwa yanzu ka fahimce alk'ila ta Kafin ya bata amsa wayarta tayi _ringing_ ya mik'e ya d'auko mata zauna inda ya tashi tsurawa sunanta da ke akan _screen_ ido a baiyane yace _suleiman_ Ras gaban raheela yafad'i saboda tun ranar da suka tafi Kaduna yake kiranta tana kin d'auka saboda batasan abunda za ta ce da shi, Amar ya mitsine ta a cinya a tsorace ta juya tana kallon sa ya d'aga mata gira yace _baby you have d call but I will never let's to received because it's your ex boyfriend_ Raheela ta sunkuyarda kai 'kasa yayin da wayar tacigaba _ringing_ Amar yayi _received_ yasaka wayar a _hand's free_ ta yadda raheela za ta ji abunda zai fad'a tun kafi yayi magana Suleiman yace haba _my heartbeat_ wane irin mumuna laifi na aikata da na chanchanci kiyi mini irin wannan hukunci mai tsauri gaske"? Kin kuwa San irin hali da nashiga a dalili rashin samu ki a waya"? Amar ya yatsine fuska yace _look_ malam Suleiman ka bude kunne ka da kyau ka saurare ni kana magana da mijinta ne a yanzu Raheela matar aure ce kuma a matsayin ka na musulmi kasan haramci ne magana da matar wani sai ka 'kiyayye domin kariya mutuncinka Cikin rawar murya Suleiman yace dallah malam kabata wayarta yaushe raheela ta zama matar aure wannan k'arya ne' Amar ya yi murmushi yasace kallon raheela ya ga tayi tsuru-tsuru da idanu yacigaba da cewa malam suleiman kenan ka ga shirgigi k'ato amma kwakwalwa ka ta yara ce, ni fa ba shawara ko umurni nake ba ka ba abunda yafaru ne nake baka labari kuma ni ba zanyi maka gargad'i akan raheela ba _Co's she is belongs to me_saidai ina maka albishir da cewa ko ka kira wayarta baza ka 'kara samu ba. Batare da yajira jin abunda Suleiman zai fad'a ba ya kashe waya ya tsare raheela da idanu ya ga tana sharar hawaye rai ya yi matukar baci ya balle murfi wayarta yaciro _sim card_ ya jefa cikin baki ya yi mata taunar _Chin gum_ ya tofar yayin da raheela ta rushe da kuka tsanani kishi ya turnuk'e Amar cikin zafin rai ya shak'e wuya 'yar banza...... [07/08 7:47 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 9⃣2⃣ Cikin hargowa yace _are you in love with him raheela_ ?? Gogaiya taku sai girgiza kai takeyi saboda babu bakin, magana Amar ya danne mak'oshi yasake wuyanta ya matsi bakinta, yace _answer my question do you love him_ ? Raheela tak'ara shiga firgici hawaye na tsiyaya daga idanu ta Amar yadaka mata mahaukaciyar tsawa yace kifad'a mini raheela kina sonshi ko"? Da kyar tace bana sonshi yaa Amar wallahi bana sonshi ka yarda da ni bantaba son wani d'a namiji a rayuwa ta Da k'arfi ya tureta ya koma ya zauna yana huci yayin da raheela ta dafe bakinta daga bisani ya mik'e ya haura sama yabar raheela dafe da baki na shiga, uku ashe yaa Amar mahaukaci ne"? Kalli yadda ya shak'e ni tamkar zai rabani da raina cab amma gaskiya _guy_ nan mugu ne dole nayi taka tsan-tsan da shi kada wata rana ya illata ni ta zabga tagumi tacigaba da tunani wannan al'amari na Amar. Yana shiga d'akinsa ya kwa6e kayansa daga shi sai _boxer_ ya shiga _bathroom_ ya yi wanka yana kamalla wanka yaduba babu _towel_ ko d'aya a _bathroom_ d'in cikin rashin damuwa yafito _nicked_ yasaka kayan bacci yafesa turare yafice har yanzu ta nan inda yabarta ko kallonta bai yi ba yanufi _darning table_ ya cika cikin sa ya 6are _lemon sweet_ ya jefa baki ya zauna bisa ga kujera da ke _facing_ d'inta a tsorace take kallonshi saboda yadawo mata _Hero_ sak ya watsa mata harara yace ke zo nan muryar ta na rawa tace Dan Allah _Hero_ kayi hank'uri, za ki zo ko za ki tsaya bani hak'uri ne"? A sanyaye ta isa gabansa tayi tsaye ya yi mata kallo sama da 'kasa sakamako rigar da take sanye da ita ya lumshe idanu, a fakace raheela take harara sa ya bude idanu yafinciko ta da 'k'arfi tafad'o kansa yace raheela kina so ki kashe ni koh"? Ta girgiza kai yace to miyasa kika yi kuka lokacin da na k'arya _sim card_ d'inki"? Ni fa bashi bane dalili kuka na To menene dalilin kukanki"? Kaine dalilin kuka na yaa Amar ka zamewa rayuwa ta karan tsaye Yad'ago fuskarta yace yanzu nan zan k'ara zamewa rayuwarki k'aran tsaye, yad'auke ta chak yanufi _bedroom_ d'insa da ita meye haka yaa Amar wallahi zanyi maka ihu barawo me ka ke nufi za kayi min"? Ya jefa ta bisa gado tasaki razanane ihu kaifa mugu ne yaa Amar ya yi murmushi yace yanzu nan zan gwada mugunta 'yar asali da k'arfi tsiya yafara _romance_ d'inta tun tana ture shi har k'arfinta yak'are sai sheshak'ar kuka takeyi ya rungume ta yana Shafa sumanta a hankali ya kira sunanta raheela tayi banza da shi yak'ara kiranta raheela ta murgud'a masa baki tace miye"? Ina sonki raheela ina tsanani sonki" Mtss....wai kai bakada wata sabuwa kalma ne sai wannan"? Ke fa shashasha ce raheela wayagaya miki kalma so tana tsofa"? _please_ yaa Amar ka kyaleni na tafi _room_ d'ina bacci nakeji Ba inda za ki je anan za ki kwana Karka tilassa ni ko kanuna mini k'arfi ka kar6i abunda bana farin ciki mallaka maka shi. Amar yayi murmushi yace ni ma banida ra'ayi tilassa ki ko nuna miki 'karfi zan jira ki ne har izuwa lokacin da, za ki kawo kan'ki gareni Raheela ta zare ido cike da mamaki tace ni Raheela Abdullahi matawalle na kawo maka kaina"? Amar ya tureta yace dallah d'agani kin wani baje bisa k'arjina sai kace kinsami katifa ,a kunya ce raheela ta mik'e zaune tana wani kakkare k'rjinta da hannaye ta, Amar yaja tsoki had'e da juya mata baya a sanyaye tafita daga d'akin ta nufi nata..... Jeeddah Aliyu🌹 [08/08 6:09 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [08/08 11:27 am] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 9⃣3⃣ Tana shiga d'akinta ta haye gado tayi kwanciya ta take magana yaa Amar tafad'o mata a rai _banida ra'ayi tilassa ki ko na nuna miki k'arfi zan jira ki ne har izuwa lokacin da za ki, kawo kan'ki gareni_ Ta kyakyale da dariya kamar mahaukaciya lallai yaa Amar bashida hankali in banda hauka ta yaya za'ayi na kai masa kaina ni da bana sonshi ta ja tsoki had'e da lumshe idanu. ```WASHE GARI``` Raheela na zauna a _parlour_ yayin da lamtana ke ciki _kitchen_ tana had'a _breakfast_ Amar yafito daga d'akin shi yana waya 'kamshi turare shi yadaki hanci ta tayi wani lumshe idanu, a zuciyarta tace ina masifar son 'kamshi turare _Hero_ ta juya ta kalli shi yana sanye da _black Jean's_ da _body hook red colour_ rigar ta d'an matsi shi shiyasa fad'ad'e k'irjinshi ya baiyana sai kace d'an _restyling_ raheela ta shak'i iska ta furza, yak'araso cikin _parlour_ ya dungure mata kai yanemi kusa da ita ya zauna yacigaba da magana da yakeyi a waya gaskiya kb kana shiga hakina haka kawai za ka dameni, da sanyi safiyar nan da zance, soyayya miye a cikin soyayya baya zafi da k'ona ga kuma d'an banza rad'ad'i ni fa kyautar zuciya ta na bayar sukuntu amma har yanzu, bansami k'ar6uwa ba shikenan zan turo maka _number_ ta amma _next time_ in kahad'u da mace ka ji kana sonta karka bari ta tafi batare da ka kar6i _number_ ta ba yana k'arasa magana ya kashe waya. Ya juya wurinta ya ga yadda ta had'e fuska ya tabe baki yace ke! Baki iya gaisuwa bane"? Ta murgud'a baki had'e da cewa ina kwana"? Harara ya galla mata, yace yana bisa gado raheela ta yi murmushi ta wani mak'e kafad'a alamar ni ko a jikina, yace ya akayi yau baki saka Jan baki ba"? Bansaniba ta fad'a kaitsaye, ke fa bakida kirki ni ke cewa bakisaniba"? To ina ruwanka da ni Ina tausayi ki raheela ranar da za ki fad'a tarko na, a yatsine tace hakan ba za ta ta6a kasance wa ba. Ni kuma nayi alqawali sai na cusa miki zazzafa soyayya ta ko ta k'arfin tsiya ce ta kyakyale da dariya had'e da mik'ewa tsaye ta wani kad'a idanu tace in kana da ra'ayi yin _breakfast_ bissmillah domin ni wannan karatu naka ba tasiri yakeyi akaina ba. Ya yi murmushi had'e da cewa wata rana zayi tasiri akanki, ta galla masa harara ta juya ta nufi _darning table_ shima ya mik'e ya Mara mata bayan sun kamalla _breakfast_ suna zaune a _parlour_ Amar ya kira sunanta _raheela_ tace _uhmm_ kinji wata sabuwa rigima da kb ya tsiro da ita wai Zainab yakeso za Ku bashi kuwa"? Raheela ta washe baki me zai hana in har ta amince da shi Amar ya tabe baki yace _okay_ zan bashi number wayarta sunyi magana, daga nan in yasami kar6uwa sai yaje yanga iyayyeta yana k'arasa magana ya mik'e tsaye yanufi k'ofar fita da sauri raheela dakatar da shi ta hanyar fad'ar yaa Amar ba dai fita za kayi ba"? Cikin zafin rai yace in na zauna gida uban me zai yi miki"? Raheela ta zaro ido maida wuk'a bawa Allah daga tambaya sai cibi ya zama k'aro Ya yi mata kallo k'asa ido dad'i na da ke raheela zurfi ciki kawai kifito fili ki ce yaa Amar jiya ka d'aura mini karatu yau kuma shine za ka fita batare da ka tunarda ni ba Raheela ta yatsine fuska tace kutt ni tun da nake da kai ko farillan alwala baka ta6a fad'a mini ba' Amar ya yi murmushi yace har musstahabai zan k'oya miki gani yadda yadunfaro ta yasa tafara ja da baya karka ta6ani yaa Amar, Dan Allah ka yi tafiyarka Allah ba ki isa ba wayace ki tsokanoni"? To kayi han'kuri ba zan k'ara tsokana ka ba ta mik'a hannu tad'auki _pillow_ kujera ta jefa masa ya tare da hannu shi ta falla da gudu ta haura sama saida ta kai _last stairs_ tayi masa gwalo Ya yi murmushi had'e da shafa sumar kanshi, a maimako tashiga d'akinta sai kawai tanufi falonshi da ke sama tafad'a kan kujera washhh ta fad'a had'e da dafe goshi, yaa Amar yana so yahad'asa mini _hypertension_ ta k'ofar baya ya shigo _parlour_ ya lallab'a ya d'ank'i hannuta yace wa na kama"? Raheela tayi narai-narai da ido tace raheela yace _Good_ ga ra da ki ka gano cewa raheela na kama to amma ae banyi maka laifi ba da za ka kamani' Kinyi laifi miye ruwa ki da ni da za ki tambaye ni fita zanyi Kana matsayi mijina kace ba zan tambaye ka ba tak'arasa magana had'e da murgud'a masa baki Amar ya zaro idanu yace yaushe na tashi daga mijin 'yar uwa ki na dawo mijinki"? [08/08 5:58 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 9⃣4⃣ Har abada kana nan a matsayin ```MIJIN 'YAR UWA TAA ``` domin ni a hakan nake kallonka ba kuma zan chanza maka matsayi ba Amar ya yi ajiyar zuciya yace banta6a gani shashasha irin ki raheela ada nake mijin 'yar uwarki kafin mutuwa ta rabamu a yanzu kuma ina matsayi mijinki. Aure mu babu haramci ko aibu a cikinsa, kafin mu mutum dubu sunyi da aure na da ke yanada matsala raheela da iyayye mu ba za su had'a mu ba saboda su ba jahilai bane karki manta raheela na aure na'eema ne ba'a haiyyaci na ba ki amince da ni raheela ni kuma na d'auki alk'awali zan ririta ki zan shayar da ke d'and'ano da gard'in _ _soyayya_ Raheela ta kyabe baki tace ni fa bance aure mu yanada illah ba, kawai abunda nakeso ka fahimta yaa Amar Kaine zuciyata bata muradi' Amar yasaki hannuta ya zauna a kusa da ita yadafe goshi, a zuciyarsa yace ya zanyi da wannan dakariyya yarinya Sam babu tausayi a zuciyarta. _Raheela_ ya ki ke so nayi da rayuwa ta"? sani kanki ne a yadda nakesonki ba zan ta6a rabuwa da ke _I can't live without you even a moment you are my life my soul, my everything please raheela give me a chance I will teacher you how to love me_ Raheela ta turo baki tace wai _Hero_ ya ka ke so nayi ne"? Ita zuciya fa ba ae mata dole, so daina tak'urani ban shirya k'ar6a tayi soyayyarka ba sai ka jira har izuwa lokacin da zuciya ta zata amince da kai. Mtss....Amar ya ja tsoki had'e da cewa anyya kuwa raheela ke mace ce"? Harara ta galla masa daga bisani tace zo ka Shafa kajiya watakila za ka gano a wane jinsi nake Da sauri ya rik'e hannaye ta da hannu sa d'aya, yasaka d'ayan hannu cikin rigarta raheela na ji saukar hannu shi inda batayi zato ba ta kurma ihu wayyo yaa Amar miye haka"? Ni fa ba 'yar iska bace da za ka dinga koya mini iskanci, ga ni yana k'ok'ari tsalaka _border_ yasa tafashe da kuka mai k'arfi gaske hakan yasa Amar yadaina abunda yakeyi, yasake mata rankwshi aka yace _next time_ in ki ka k'ara cewa na Shafa to gaba d'aya zan shafe ki Raheela ta zame daga kujera ta zauna 'kasa tana sauke numfashi zuciyarta cike da haushi Amar Ya mik'e ya tsaye yana mata dariya yace, ni zan fita ina fatar za ki haddace wannan karatu saboda akwai Sabon _topic_ da dare kuma zafin wannan zafi, ya yi mata gwalo yafice. Yayin da raheela tak'ara harzuk'a a baiyane tace ashe in ranka yana 6ace akayi maka gwalo zafi ne da shi dama haka umma hajara ta keji duk lokacin da nayi mata gwalo"? shiyasa takeji kamar ta yanka ni ta rufe idanu ta kamar mai jin bacci tasoma tunani abunda yawakana, tsakanita da yaa Amar nan take taji wani abu yana safa da marwa a jinita ta dafe k'irjinta had'e da furta na shiga uku shin me wannan sabon sauyi da nakeji yana shigata yake nufi"? ```WAIWAYE ADON TAFIYA``` _A GARI KADUNA_ Tun safe umma hajara ta shirya tana jiran aunty asabe, ta zo su d'auki hanyar _Enugu_ domin ta kagara ta ganta gaban sabon bokan saboda yadda ta ji aunty asabe take zuzuta shi tabbas shi kadai zai iya tarwatsa mata rayuwa raheela, ta kad'a kai had'e da kyaci ta sha ji labari boka Edulo a baki aunty asabe tsohon iyamurai ne ko hausa bayaji saidai buroki matsifi ne na gaske wayarta tayi _ringing_ shine ya yi sanadiya dawowar ta daga duniya saka mugun nufi da sauri tad'aga tace haba aunty asabe tun dazu na shirya ke kadai nake jira, sai kuma naga umma hajara tayi shiru daga bisani ta kurma ihu ta jefar da waya tacigaba da kururuwa had'e da gunji kuka Abba da Aunty amarya suka shigo d'akin nata agigice aunty amarya ta dafa ta tace me ke faruwa ne hajara"? Cikin gunji kuka umma hajara tace na shiga uku na lalace Sadeeya...... Jeeddah Aliyu🌹 [09/08 8:52 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [09/08 12:44 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 9⃣5⃣ Abba yadaka mata tsawa yace wai ba za ki fad'a mana abunda ke faruwa ba"? Umma hajara tak'ara kwatsama ihu had'e da zubewa k'asa Abba yarik'o ta yace dad'i na da ke hajara rashin takwali ko ma menene yafaru ya kamata ki saka hank'uri da dangana a zuciyarki da kyar ta bud'e bakinta tace shikenan narasa iyayye na lami da alhajimu gobara ta cinye su a tsorace Abba da aunty amarya suka d'auki kalma shahada, daga bisani Abba yadawo lallashinta ya juya wurin aunty amarya yace ki je ki fad'awa saura mutane gida su fito mu tafi. Allah sarki duniya umma hajara na yunk'uri kassara rayuwa raheela, sai kuma ga wani babban al'amari ya cika da ita gobara ce ta tashi a tsikiyar dare d'an Tsoho da tsohuwa suna ciki sharar bacci suka ji hayaki ya turnuk'e gida kafin akawo musu d'auki har wuta tagama aikinta sai, gawawaki su aka fito da su umma hajara tarasa 'yarta na'eema ga shi kuma tak'ara rasa iyayyeta a lokacin guda shin ko hakan zai sa tayi nadama ta tuba ta komawa Allah tun kafin ta, ta mutuwa ta riske ta"?? ```ABUJA``` Tun lokacin da Amar yafita yabar raheela cikin halin tilawa darasi da ya koya mata, _mtsss_ ta ja tsoki tasoma zance zuci gaskiya _Hero_ yana so yajefa ni cikin wani hali kalli tun lokacin da ya mammatsi ni yafita narasa sukuni sai wani d'an banza _electric shock_ nakeji yana yawon a jinina, lallai in haka tacigaba da wanzuwa a tsakani mu tofah babu makawa zan fad'a a tarko da _Hero_ yakafa min. _Na shiga uku ni raheela zan tafka abin kunya ```SON MIJIN 'YAR UWA TAA``` zai kamani ina zan kai alqawali da na d'aukawa yaya na'eema_ ?? Wasu zazafa hawaye Suka tsatsafo daga idanu ta, kai ina wallahi ba za ta sabu ba wai bindiga a ruwa tabbas ba zan bari makamai _Hero_ suyi tasiri akaina ya Zame mini dole na tanadi makamai Kare hari domin na kare kaina daga duk wani hari da yaa Amar zai kawo min matukar nayi sake yagano nafara zurmawa sunana _margaaya_ {Ta bakin indiyawa lol} Kamar daga sama taji sautin lallausar murya sa saitin kunnenta, yace _raheelaaah_ a tsorace tad'ago had'e da furta _oh my God you scared me_ Amar yasaki murmushi ta galla masa harara yaushe ka shigo _parlour_ nan kuma me kadawo yi"? Tun lokacin da kika Lula duniyar sama kina tunani _Hero_ tun a lokacin na shigo sannan kuma zuciyata ce tafad'a mini kina tsanani buk'atuwa da son ganina da alama darasi na yafara tasiri shiyasa nadawo na d'an k'ara tunatarda ke _are you not happy_ ?? _I'm not_ tafad'a tana murguda baki Ya mak'e kafad'a alamar ke kika sani yak'ara matsawa daf da ita har yana jin bugawar zuciyarta ya yi 'kasa da murya yace to me kike tunani"? Wannan kuma bai shafeka ba tsakani na ne da zuciyata, na tsani shishigi da cusa kai ba kwarjini a rayuwata kai kuma ka kwarai a wannan fagge Sai kayita shshigewa mutane, ba kuma shi zai sa kasami gidin zama anan ta nuna saitin zuciyarta da yatsa. Duk da zuciya Amar ta Sosa da jin kalamai ta amma sai yadake, kamar ba abunda ya ji, batare da yace uffan ba yajuya yashige _bedroom_ d'insa, raheela tasaki ajiyar zuciya tace amma _guy_ nan bala'i ne mutum sai kace aljani saura kiris ya halbo jirgina, k'amshi turare _pure blue_ yadaki hancinta shi yabata tabaci yadowa cikin _parlour_ da sauri ta yada kallonta a bakin k'ofa idanu ta suka hasko mata shi, cikin lallausar farar shadda tasha aiki da bak'in zare 'kafarsa sanye da _cover shoe black colour_ yana rik'e da hularsa bak'a yana gyara mata kari a zuciyata tace cab amma _Hero_ mugun d'an duniya ne ko ina yanufa da yasha wankan farar shadda"? A baiyane kuma sai tace _iyeee d'an guyu ina kuma aka dosa da farar shadda_ ?? Harara ya watsa mata yace bansaniba Uhm...Allah yasa wannan wanka ba don mata waje ake yi sa ba don ni bangane ba wai anyi yamma da kare. Amar ya yi d'an bazawari murmushi had'e da cewa dad'i na da ke raheela shirme ni da nakeda zankad'ed'iya mace irinki me zai had'ani da matan waje ae ko sha'awarsu takamani saidai nadawo, gida na huce gajiya a jikinki yak'arasa magana had'e da d'aga mata gira. Raheela ta kwa6e fuska tace tir kai kan Sam bakaji kunya furta irin wadanan magaganu. Amar yace ke karki 6ata mini lokacin da wannan d'an banza surutu naki kamar _parrot_ Kaduna zan je ta'aziyya Allah ya yiwa iyayyen umma hajara rasuwa ga shi ke kuma kin tsare ni da surutu. _innalillahi wa'inna illahi raji'um_ raheela tafad'a had'e da dafe 'kirji tace yaa Amar _accident_ sukayi ne"? Ya girgiza kai had'e da cewa a'a gobara ce ta tashi tsakiyar dare su duka biyu sun kone a yanzu haka har anyi jana'izza su. Cikin tausayawa raheela tace ashe tafiya kaduna yasamemu Kallon sama da k'asa Amar ya yi mata ya wani ta6e baki yace.... [09/08 6:18 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 9⃣6⃣ Tafiya _Kaduna_ tasame ku, ke da wa 'yan mata kaka"? Raheela ta turo baki tace ni da kai mana' _Uhm....yarinya ce Allah kin tuba kare hauka ya cije ni da zan tafi da ke Kaduna_ ?? Ae ba sa6o nayi ba da za kace na tuba tak'arasa magana tana murgud'a baki Ko kinyi sa6o ko bakiyi ba ba zan je da ke ba kwata-kwata kwana ki uku kachal a gidanan shine zan d'ebe ki zuwa _Kaduna_ Idanu ta taf da kwala tace dan Allah yaa Amar katafi da ni ae ka ga bai dace ace banje na yiwa umma ta'aziyya ba"? Amar ya ta6e baki ya yi tafiyarshi raheela ta kifa kanta a hannu kujera tana gunji kuka, har Amar ya kai bakin k'ofa sautin kukanta yadaki kunnensa, kasa jurewa yayi yadawo falon ya durk'usa gabanta yad'ago fuskarta yace kinsan duk duniya ba abunda yake k'ona mini rai irin kukanki banaso _please_ raheela kidaina yi mini hasara hawayenki tashi maza ki shirya mu tafi Farin ciki ya lullu6e raheela ta mik'e da sauri ta nufi hanyar d'akinta tana is a bakin k'ofa Amar, ya kwada mata kira tayi tsaye chak yak'araso daf da ita yace ki tabbata kin Saka Jan baki{lipstick} Zaro idanu tayi had'e da furta ni da zan tafi gidan mutuwa miye had'i na da Shafa Jan baki {lipstick}"? Matukar kinaso na tafi da ke dole kibi umurni na batare da tace komai ba tashiga d'aki ta sauya kaya zuwa atamfar _super Holland_ _red &yellow colour_ anyi mata d'ikin _cut lace_ kayan sunyi masifar yi mata kyau tayafa _yellow veils_ had'e da takalmi ta _hill_ su ma _yellow colour_ tafesa turare tayi tsaye gaban _dressing mirror_ tana kallon kanta ta ga yadda tayi kyau tasaki murmushi, sai kuma ta6ata fuska sakamako tunawa da umurni yaa Amar da tayi, tad'auki _lipstick red colour_ tashafa tafice daga d'akin har yanzu yana nan tsaye inda tabarshi, ya kafe ta da idanu kamar yau ne yafara ganinta ta watsa masa harara had'e da cewa wannan kallo duk na menene"? Amar ya lumshe idanu yace na yabawa ne kin yi matukar kyau kamar na cinye ki. Raheela ta6ata fuska tace uhm...tace ka ji da shi a _parlour_ suka tararda lamtana tana 'yan goge-goge ta Amar yace lamtana za mu tafi Kaduna ki kula da gida insha Allahu da yamma za mu dawo, lamtana tace Allah ya dawo da ku lafiya a gaida su mami. Raheela tace za suji Amar yana gaba tana biye da shi har suka isa _parking space_ ya bude mota yashiga raheela aka kame _seat_ d'in gaba Amar ya yi addu'ar hawa k'arfe ya tayarda mota _Joseph_ ya bude _gate_ tun lokacin da suka d'auki hanya ba Wanda ya tankawa d'an uwansa kowane da abunda yake sak'awa a zuciyarsa a dai-dai wani k'ato shago na siyar da wayoyi {phone's} Amar ya yi _parking_ batare da kalli ta ba yace ina zuwa ya bude k'ofa yafita yayin da ita kuma tabishi da kallo har yashiga shagon tana kallonsa, tasauke gwaron numfashi cikin zuciyarta tace yanayi tafiyar _Hero_ kadai abar sha'awa ce gaskiya _Hero_ yahad'u ba k'arya sai kuma ta wani turbune fuska saidai matsala ta da shi miskilanci da shu'umaci ga shi kuma mugu, k'arar bude k'ofa yasa tajuya ga ni shi tayi rik'e da Leda fara mai d'auki da tambari shago da yashiga yana shiga mota don tsabar d'aukar magana irin na raheela tace _Hero_ ya yi banza da ita kamar baiji ta kira shi ba, yaja mota sai da ta galla masa harara sannan ta bud'e murya da k'arfi tace _Herooo_ taka wawa birki yagangara gefen titi ya yi _parking_ ya cije lebb'e sa ya na mata kallon k'asa ido kallon da raheela ta tsana kenan a kasalance ya furta _baby_ ya akayi ne"? Wani duba tayi masa tana murmushi nan take Amar yagano wani sabon iskanci za ta guma masa yayinda shi kuma yasoma shirya mugunta da zaiyi mata yace kiyi magana mana kin wani tsaya kina murmushi munafuci. Raheela ta turo baki had'e da cewa..... Jeeddah Aliyu 🌹 [09/08 8:53 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [09/08 7:59 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 9⃣7⃣ Na ganka da Leda shine nace _gift_ d'in amarci ne kasiyo min saboda ko 'yar kaza nan da ake siyawa amare baka siyo mini ba"? Amar ya yi murmushi yace yanzu nan kuwa zan baki _gift_ dama kinsan nace ki Shafa _lipstick_ kinga sai na tsotsi kayana sai na baki _gift_ kazar amarci kuma tana nan tana jiranki duk ranarda kika shirye ki kai, kanki _bedroom_ d'ina za ki ci kaza sai kinture ya k'arasa magana had'e da kashe mata ido Ras-ras gaban raheela yafad'i tasoma danasani furtawa Amar wannan tambaya kafin tadawo daga duniyar sak'e-sak'e Amar yafisgo ta ya had'e bakinshi da nata yana saida ya tsotsi _lipstick_ d'inta tass sannan yasaketa yayinda raheela ta jigina jikinta a jikin kujera tana sauke numfashi Amar yalek'a fuskarta yaga ta lumshe idanu ta, yad'auki Ledar yajefa mata a cinya ya zura hannu cikin aljihu gaban rigarsa yaciro wayarta yad'aura mata saman ledar yaja mota cikin nishad'i. Saida raheela ta share tsawon dak'ik'a biyar sannan ta bud'e idanu ta karo na farko da raheela bataji haushi abunda, Amar ya yi mata amma tsabar tauri rai da kafiya irin na raheela sai kawai tace ni fa gaskiya yaa Amar nafara gajiya da wannan al'amari naka ta yaya kake so mayarda ni kamar _lollipop_ na fad'a maka bana sonka na tsane ka miyasa bazaka fitarda ni daga zuciyarka wallahi duk ranarda ka k'ara tsotsa mini baki sai na sharyarda kai mamaki har tagama zabga iya shegenta Amar bai dube ta ba _driving_ d'insa kawai yakeyi kuma babu alamar ya ji zafin maganarta mamaki yarufe raheela cikin zuciyarta, tace miyasa duk zafin wadannan magaganu da na furtawa _Hero_ bai nuna ya ji zafi ba"? Ta yi shiru tana sak'e-sak'e ko ta bashi hank'uri sai kuma ta wata zuciya tace da ita kina bashi hank'uri zai fara tunani ko kinfara sonshi take raheela ta turbune fuska sai wani cika take tana batsawa har suka shiga garin Kaduna ba Wanda yak'ara kula d'an uwansa kuma raheela bata bude Leda da yabata ba kaitsaye Amar unguwar da iyayyen umma hajara suke da yake gidan yayan umma hajara Alhaji sadi ake zaman mak'ok'i saboda babu nisa tsanani sa da gidan mahaifin nasu Alhaji sambo Amar ya yi _parking_ batare da raheela ta kalle shi ba ta bude murfi mota tafita tana shiga falon gidan suka had'a ido da umma hajara cikin sanyi jiki raheela tak'arasa wurinta, tayi mata ta'aziyya a dak'ile umma hajara ta amsa raheela ta sada kai k'asa tanaso ta tambayi umma hajara mami da aunty amarya tana jin tsoro irin amsar da za tabata. Amar ya shigo falon ya durk'usa ya yiwa umma hajara da sauran mutane falon ta'aziyya shima umma hajara ta amsa ba ya6o ba fallasa, daga bisani Amar ya mik'e yafita, don tsabar jarraba da rashin imani irin na dangin umma hajara saida suka yadawa raheela magana aunty asabe tace hajara wannan kamar amarya raheela"? umma hajara ta kyabe baki had'e da cewa ba kama bace ita ce mai auren cin amana Aunty asabe tace ikon Allah kwana uku da aure ace amarya tafito anyya kuwa hajara wannan 'yar taku, takai budurcinta gidan Amar"? A tsoroce raheela tada'go idanu ta cike da kwala ta tsurawa umma hajara ido taji irin amsar da za ta bata.... [09/08 8:50 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 9⃣8⃣ Umma hajara ta yatsine fuska kamar gwaggo biri tace wane irin budurci"? Ae tun a waje Amar yakawar mata da budurci babu abinda batasaniba domin ko zaman da tayi gidansa, a lokacin da na'eema tana Raye ba abinda suke aikatawa sai masha'a wannan tsinaniya da kike gani tuni Amar yagama kwalkwale ta ya tsotsi ta ya gama kwashe albarkatu jikinta. Aunty asabe ta wani zaro idanu na munafuci da kilinbibi tace biri ya yi kama da mutum shiyasa aure da kwana uku tafito don ta nunawa duniya tagama sani dad'i da d'and'ano d'a namiji. Wata mata da takasa kunne tana sauraro abunda ke wakana, tayi karaf tace gata yarinya k'arama ace kinsan d'a namiji tir da ke iyayyenki sunyi hasara haihuwa ana magana kina fik'i-fik'i da idanu 'yar banza mai idanu kamar fitila _vespa_ Umma hajara tace wannan tsohuwar kilak'i ce yarinya wannan k'ato da ki ka ga tafiya shine aboki lalatar ta tsabar yasan dad'inta ya kashe 'yar uwa ta ya aure ta. Aunty asabe tace kice ```mijin 'yar uwa taa ``` ta aura kwarai kuwa umma hajara tafad'a tacigaba da cewa bak'ar algguma shegiya tsananiya sai na zama ajalinki tashi Ki ba mu wuri sai faman wari k'ato ki keyi Raheela ta fashe da matsanacin kuka, mai matukar cin rai ta tashi tsaye da jiri na d'ibar ta tanufi k'ofar fita saura mutane da ke cikin falon da basuji abunda ke faruwa ba sai faman bata hak'uri sukeyi a tunani su kukan mutuwa takeyi Amar na zaune ya hango raheela tafito tana kuka, tashiga mota hankalinsa yayi masifar tashi da sauri ya mik'e yanufi mota takifa kanta tsakiyar cinyoyinta tana gunji kuka, cikin sark'ewar halshe Amar yace..... Jeeddah Aliyu🌹 [11/08 6:53 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [11/08 8:23 am] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 9⃣9⃣ Meke faruwa ne Raheela kike kuka"? Tacigaba da rusa kukanta mai cike da bacin rai da k'onar zuciya tamkar, bataji tambayar da ya yi mata ba. Cike da sanyi jiki had'e da alhini sanadi kukanta ya jawo ta cikin jikinsa, cikin sigar rarrashi yake magana _please raheela talk me_ miye musanbabi kuka ki"? Nan ma raheela bata tanka ba saida tad'ago rinannun idanu ta ta dubi Amar tak'ara rushewa da kuka' Amar yakara rud'ewa yace haba raheela na tambaya ki kin kasa bud'e baki ki bani, kuma kink'i daina kuka yakikeso nayi da rayuwata"? Na tsani kukanki raheela yana jefa ni a yanayi na tashin hankali, na rok'e ki da ki share hawayenki saboda zubar su tamkar ana zubawa zuciyata tafasashe ruwan zafi ne. Kuka yaci k'arfi raheela da kyar ta sarafa halshenta tace _please yaa Amar mu bar gidanan banaso na sake bud'e idanuwa na naganni a cikin sa Mamaki ne ya sark'e Amar har yahadasa masa zaro idanu batare da yace komai ba yabi umarni ta ta hanyar fisga mota aguje, _driving_ yakeyi amma hankalinsa na kan raheela domin har yanzu kuka takeyi yana _parking_ raheela ta balle murfi mota, tafita da gudu tanufi _part_ d'in kaka, yayinda Amar ya yi mutuwar tsaye daga bisani ya Mara mata baya, kaka na kishigide a _parlour_ ta tana tauna goro raheela ta shigo aguje tafad'a jikinta tasaki mai k'arfin gaske dama ga raheela ta kware da kukan yankar kauna musanmman da taji a jikin kaka ae kuwa kaka ta rud'e matuk'a tace na shiga uku me zan gani haka raheela daga ina ki ke kardai wannan d'an banzan, narka ki yakeyi don wallahi Amar ba tausayi ne da shi ba. Amar da ke tsaye a bakin k'ofa yayi karaf yace da yake ni ne mareni ki karkataciya kuuka mai dad'i hawa duk wata shara da ki ka kwaso kaina kike juyewa, to a wannan karo bani bane asalima bansan dalili kukanta ba sai ki tambaye ta tafad'a miki ke da kike da tausayi shugaba ta kungiyar talafawa marayu. Harara kaka ta galla masa girar idonta ta mik'e tayi cirk'o-cirk'o tsan-tsan masifa da bala'i da aka jima ba'a ta6a ba ya motsa tace ta yaya ya za Ku tare sannan kace bagada masaniya akan kukanta ko kuma so ka keyi ka raina mini hankali"? Kinga kaka karki sauke kwadon masifa da bala'i ki akaina yadda ki ke jin zafi da rad'ad'i kukanta nima haka nakeji K'arya ka keyi Amar kasan dalilin kukanta kawai dai ba zaka fa'da ba saboda kasan ka zalunce ta. _how many time kaka I told you I don't known anything about her cry_ ki tambaye ta da kanki _maybe_ ke ta fad'a miki. A hazuk'e kaka tace kai Amar ka kiyayeni, shine ka juye baki kana turanci ka na banza da wofi to magafok yaci uwarsa Amar ya rufe baki had'e da zaro ido yana kallon kaka, tun lokacin da aka fara buga wuta tsakani Amar da kaka raheela tadaina kuka tana sauraro su, gani za ta kwa6e musu yasa tace ni fa kaka, ba abunda yaa Amar ya yi min kuma baisan dalili kuka na ba. _thank God_ Amar yafad'a had'ewa da zaunawa yace yanzu sai kifad'a mana dalilin kukanki, raheela ta sada kai k'asa ta fed'e musu daga biri har wutsiya ae kuwa kaka tasoma zazzga tijara da yanka kauna saida tagaji don kanta tayi shiru Amar kan dafe goshinsa ya yi ya kasa cewa komai daga bisani yad'ago yace Dan Allah kaka karki yiwa umma hajara magana, saboda irin wannan babbar magana za ta iya haddasa fitina musanman in Abba ya ji domin zai iya d'auka mumuna mataki akanta. kaka tace me zai sa nayi mata magana ae duk abunda mutum ya yi don kansa jahilci ne yake dawainiy da ita har yanzu watan nadama ta ne bai tsaya ba amma a juri zuwa da tulu rafi waya zai fashe. Amar ya yi murmushi had'e da cewa, tashi mu tafi _part_ d'in su mami mu gaida su daga nan mu wuce kinga mu bar lamtana ita kadai Raheela ta narke fuska kamar za tayi kuka, da sauri kaka tace tashi Ku tafi 'yar albarka raheela ta mik'e tana murmushi, Amar kuma ya tabe baki kaka tace ina zuwa bara d'auko miki aya cikin zumudi raheela tace aya mai sikari kaka"? Kaka tace eh! Har kaka tadawo Amar yana aikawa raheela harara ita kuma tana murgud'a masa baki, kaka ta mik'awa raheela leda aya suka fice, kaitsaye part" d'in mami suka fara shiga mami tayi matuk'ar farin ciki gani su tak'ara yi musu nasiha dangane da zaman aure daga bisani sukayi mata sallama suka shiga part" d'in aunty amarya, sun tararda da ita zaune a _parlour_ da gudu raheela tafad'a jikinta, aunty amarya ta tureta had'e da daka mata tsawa ke miye haka"? Wai yaushe za kiyi hankali maama ki gano cewa girma yakamaki kidaina wannan shashaci naki? Raheela ta turo baki Amar ya gaida aunty amarya ta amsa cikin sakin fuska, raheela tace gaskiya ni banta6a gani _last born_ mai bak'in jini iri na abunda ki keyi min aunty ko su yaya Abdul da suke _first born_ bakiyi musu haka nan tak'arasa magana hawaye na zuba daga idanu ta, aunty amarya tayi murmushi had'e da jawo ta a jikinta tace !haba raheela kaka miye kuma abin kuka"? Cikin sigar shagwaba raheela tak'ara narkewa ajikin aunty amarya Yatsine fuska Amar ya yi had'e da mik'ewa tsaye yace to sarki shagwaba sai ki tashi mu tafi, ba yadda raheela dole ta mik'e suna shiga mota raheela ta d'auki leda da Amar yabata had'e da cewa bara naga miye a cikin wannan Leda da aka yiwa kirari da _gift_ d'in amarci in naga ba wani abin a zo a gani bane a fuska zan jefawa mutum kayansa. Sau d'aya Amar ya dube ta ya kauda fuska....... [11/08 11:51 am] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 1⃣0⃣0⃣ Raheela na bud'e Leda taci k'aro da tsaleliyar waya {phone} mai matukar kyau da tsada ta kurma ihu farin ciki ya lullube ta batasan lokacin da ta rungume Amar mahaukaci birki da Amar yataka yasa raheela ta dawo natsuwarta, inda Allah ya taimaka basu hau kan titi da sun had'a d'an 'karami accident{hatsari} Amar Yasauke gwaron numfashi yarike kunne raheela ya murd'e yace ke so kike mu yi accident {hatsari} koh"? Kallon mamaki ta watsa masa daga bisani tace don nayi ihun farin ciki shi ne zai sa mu yi accident"? _uhm_ tsanani dad'in wannan _hot hug_ da kika bani shine ya kusan haddasa mana _accident_ bakiji wani irin masifafe _shock_ da ya ratsa jinina saura kiris nasaki _steering_ Ta dage gira sama ta yatsine fuska tace, gaskiya yaa Amar kai maye mata ne kawai na d'an rungume ka sai ka susuce, ni fa ba da wata manufa nayi ba nayi ne don na nuna maka farin cikin siya min waya{phone} da akayi. Amar ya lumshe ido yace raheela kenan mata ababe so ne duk wanda yace miki bayaso mata k'arya yakeyi don bai samu bane, ballatana ni da nakeda _fresh & sexy girl_ irinki ni da za ki taimaka ki k'ara min guda d'aya ni kuma nayi miki alk'awali zan siya miki _lollipop_ Ta zaro ido fuskarta ta baiyanar da tsoronta a fili daga bisani tace me zan k'ara maka"? Yayi k'asa da murya yana wani lum-lumshe idanu yace _hot hug_ kafin raheela ta bashi amsa ya manna ta a k'irjinsa ya rungumeta tsam a jikinsa yana shinshina had'e da shak'ar k'amshi sai wani sauke zazzafa numfashi yakeyi, tuni yafara fita hayyacinsa raheela ta tak'ark'are ta damkara masa cizo a wuya baisan lokacin ya saketa ba yasaki ihun azaba, yayinda raheela tasoma kiciniyar mayarda _zip_ d'in rigarta saida Amar yad'auki tsawon _5 minutes_ yana jinyar wuyansa daga bisani yasake mata rankwashi yace mayya kawai wance bataso farin cikin mijinta, in ba dole ba me zanyi da mace irinki k'irji a bushe kamar kilishi tab'a ki kawai nakeyi ba abunda nakeji mata-maza kawai. Ta juya a fusace ta dube shi ta nuna shi da yatsa idanu ta sun kad'a sunyi jajir tace k'arya kake yi yaa Amar ka kira ni da suna mata-maza da bakaji komai da baka dinga tab'ani ba, kuma wallahi sai kayi nadama kira na da wannan sunan. Ya kalle ta ya kawar da kai yayinda ya ja mota yana dariya k'asa-k'asa abunda yak'ara k'ula da raheela kenan tace kaga malam kayi dariyarka iya son ranka nima lokacina na zuwa _I will take my revenge_ Amar ya kyakyale da dariya har yana dukan _steering_ daga bisani ya tsagaita da dariya da yakeyi yace _you are such a fool raheela_ ba abunda za ki iya raheela tayi shiru tana tunani lallai sai na nunawa yaa Amar ni cikkiya mace ce ba mata-maza ba sai na haddasa masa rashin baccin da ciwo kai ta juya ta dube shi tana wani cize lebb'e tayi murmushi kawai da wannan _drama_ suka shiga garin _abuja_ Da yake kowane su yadebo gajiya suna Shiga cikin gida kowane yanufi _room_ d'insa. ```BAYAN SATI D'AYA ``` kasancewa yau _weekend_ ne Amar bai cika fita ba sai in fitar ta zama dole, yana zaune a _downstairs parlour_ yana sanye da wando _three quarter_ da Riga marar hannu {armless}ta d'an yi _tight_ d'insh hannu shi rike da _newspaper_ ta _daily trust_ yana dubawa lokaci-lokaci yakan mik'a hannu shi, bisa _stool_ d'in da ke gabansa yad'auki gwagwani _Amstel Malta_ yana _sipping_ 'kamshi turareta ya sauka a hancinsa ya lumshe idanu, cikin zuciyarsa yace wannan 'yar Bana bakwai sai yanzu tagama dama tashi"? Ya juya dube ta tasha kwaliyya cikin _English wear's_ wando _skintight blue colour_ da _top whites colour_ a gabanta a rubuta _Hot_ da _blue colour_ rubutu a lokacin gud'a Amar ya hadiye yawu had'e da sauke sanyaya ajiyar zuciya domin wanka raheela yagama tafiya da imani shi da sauri yad'auke idanu shi daga kanta. A hankali tak'araso wajensa tayi tsaye tana kallon sa batare da ya dube ta ba yace wannan wane irin sabon fi'eli ne kin wani tsaya min akai"? Tasaki murmushi mai sauti tace to bara na dawo gabanka, tadawo gabanshi yayinda numfashin Amar yafara fita da sauri -sauri tsanani sha'awarta ta kamashi.... Jeeddah Aliyu🌹 [11/08 6:54 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [11/08 3:50 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 1⃣0⃣1⃣ Har Amar ya mik'a hannu ya yi mata kamu kazar kuku sai kuma yadakata sakamako sautin kukan, lamtana da ya karad'e _parlour_ a tsorace suka nufe ta Kowane su yana tambayar ba'asi kuka nata da kyar ta bude baki tace yanzu nan yayana ya kirani a waya yace inna ta batada lafiya sosai shine nace bara na fad'a muku ina so in tafi k'auye yanzu nan saboda bansan wane hali take ciki ba. _subhanalillah_ Amar da raheela suka fad'a a lokacin d'aya Amar yace Allah yabata lafiya yasa kaffara ce Raheela ta amsa da _Ameen_ Amar yacigaba da fad'ar ki je ki had'o kayanki mu kai ki _motor park_ {tashar mota} ke kuma raheela ki je chanza kaya tuni lamtana tanufi d'akinta yayinda raheela ta juya a sanyaye, zuciyarta cike da tausayi lamtana. A maimako raheela ta chanza kaya sai kawai tasaka _after dress_ tad'auki _phone's_ d'inta tafito, lamtana na tsaye tana sharar hawaye raheela tace kidaina kuka lamtana insha Allahu inna za ta sami lafiya lamtana ta d'aga kai Amar yafito hannu shi rik'e da _car Key's_ suka fice, motar da Daddy ya ba raheela ita suka shiga, bayan su ajiye ta a _motor park_ Amar yafito da kud'i 'yan _0ne thousand_ na _20 thousands_ yabata yace ga wannan ki siyawa inna magani yak'ara Ciro _five thousands_ yace wannan kiyi kud'in mota Allah yabata lafiya. Lamtana tasaka hannu biyu takar6a tace na gode likita Allah yasaka da alkhairi Allah yabiyaka yak'ara bud'i na alkhairi.{```Ameen```} Raheela ta rik'o hannuta tace ki gaida inna da jiki sai mu yi waya suna kallo lamtana tashiga mota. Daga bisani suka shiga mota suna bisa hanya, cikin sigar shagwab'a raheela ta kira sunan sa ta hanyar cewa _Hero_ Ya akayi ne _Miss hot_ ? Ji suna da ya kira ta da shi yasa tasaki murmushi mai sauti tace yau kuma wani sabon suna nasamu"? _umhh_ ko baiyi miki dad'i bane"? Ya yi min mana baga har da murmushi yasubuce min sakamako dad'i sa da ya ratsa ni. Amar ya yi mata kallon ke 'yar duniya na fa gano ki akwai abunda kike nema a wurina a baiyane kuma yace yi maganarki inajinki Tayi k'asa da murya cikin tausasa halshe tace me zai hana mu zaryace wajen k'oyon mota ka koya min tun da yau _weekend_ ne baka aiki komai ya tabe baki yace yau kuma rigima da kika tsiro da shi kenan"? _please yaa Amar Dan Allah za kayi ba don ni ba. Ae dama don Allah nake zaune da ke don banga abunda nake k'aruwa da shi a tare da ke !Haba _Hero_ bakinka bai kamata yafad'i haka ba, tafad'a had'e da langwabe wuya _mtss_ yaja dogo tsoki mai cike da jin haushi yace uban me kike tsinana min sai faman wahalar da zuciyata kike yi kin hanani abunda yake halak-malak d'ina wallahi ina tausaya miki raheela duk ranar da kika shiga hannuna sai nafashe duk wata wahala da kika dinga bani. Don kawai nace ka koya min mota shine za ka dinga furta zafafa maganganu to Allah yabaka hank'uri ni banaso fitina. Batare da Amar yace komai ba yanufi filin koyo mota tun daga ranar yadinga koya mata _driving_ cikin sati d'aya hannuta ya kware da _driving_ Raheela na tsaye a _kitchen_ tana had'a musu _breakfast_ zuciyarta cike da tunani yadda cikin d'an k'ank'ani lokacin ta kamu da zazzafar soyayya yaa Amar saidai ta k'udiri aniya boyewa yaa Amar saboda bataso ya yi sauri gano ta zurma a tarkonsa amma zahiri gaskiya son Amar yana matuk'ar wahalarda ita sai kawai ta tsince kanta cikin nishad'i dama haka takeji a duk lokacin da takasance cikin tunani sa, gani tunani ba zai zame mata mafita sai kawai takama rera wak'a ciki murya ta mai dad'in sauraro _sirrina zuciya in zaka tona ganinan ma'anar soyayya ta kabi tsarinaa_ a hankali yake sand'a yana karasowa daf da ita ya rungumeta, ta baya yasaka kanshi a tsakiyar wuyanta yana shinshina ta raheela tasaki ajiyar zuciya... [11/08 6:52 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 1⃣0⃣2⃣ Amar yak'ara matsita cikin k'irjinshi tasaki 'yar k'ara washhh sanadi da yak'ara rura wuta sha'awa Amar motsawa, cikin rikitaciya murya yace _baby menene tsari naki? a shirye nake da na bisa matuk'ar za ki yarje ki amince na toni wannan zuciya taki ni dai burina na mallaki soyayyarki_ Raheela tayi murmushi tace _Hero_ kenan kai dai baka rabuwa da rigima kadaina gani ina kiranka da _Hero_ kayi tsanmani, jarumta ka takai matsayin da za ka tona zuciyata tayi wani girgiza kai. Amar ya yi murmushi yajuyo da ita suna _facing_ d'in juna yace k'arya kike yi raheela tuni nagano cewa na tone zuciyarki har na kafa sansanina a ciki kawai yarinya ki bada kai had'in kai na shayar da ke zuma soyayya wance har abada dad'i da zaki had'e da d'and'ano ta ba zai ta6a gushewa a bakinki yak'arasa magana had'e da shafar _lips_ d'inta da d'an yatsa. Ture shi tayi tace dallah sakeni banaso irin wannan d'abi,a taka Amar ya yi k'asa da murya yace _please raheela ki taimake ni wallahi na kai k'ololuwa a sha'awarki karki jefa ni cikin wani hali_ Raheela ta yi shiru tana nazari magaganu sa Amar nagani tayi shiru sai ya yi tunani ko ta amince ne nan take ya kashe _gas cooker_ yayinda raheela ta bishi da kallo, tana mamaki me Amar yake yunk'uri aiwatarwa akanta. Kafin tadawo daga duniyar tunani ya d'auketa chak kamar 'yar tsana, yanufi _downstairs bedroom_ saboda a yadda yakeji ba zai iya hawa _upstairs_ ba bai ta6a jin sha'awa raheela irin yau. Raheela sai shushure takeyi da k'afafu ta, had'e da rok'o sa Dan Allah yaa Amar ka kyaleni kai fa kace ba za ka tilassa ni ko kayi min da k'arfi shine yanzu za ka sab'a alk'awali. Amar bai saurare ta ba sai da yaga yasada ta da gado ya balle _buttons_ d'in rigarsa yasoma _romance_ d'inta ta ko ina aika mata da dafin _kiss_ yakeyi da sauri ya cire mata riga ya jefarda ita k'asa take abunda yafiso da kauna ya kuma jima yana nema irin wannan damar suka baiyana a gigice ya chafke su, yana sarafa su ta yadda yakeso, yayinda raheela wani abu yafara yawo a kwakwalwa raheela ta tuna da waye Amar ta tuno cewa shi fa ```mijin 'yar uwa taa``` ne matuk'ar tayi sake Amar yasami biyan buk'atarshi shi kenan ta k'arya alqawali da ta yiwa yaya na'eema tafashe da wani mashahuri kuka ta d'ad'age iya k'afinta ta ture shi, da yake yariga ya yi nisa ba wani k'arfi ne da shi tace bana sonka, bana sonka yaa Amar na tsane ka matuk'ar karabani da budurcina ba zan ta6a yafe maka mugu kawai. Amar ya tsaya chak yana sauke numfashi, haushi da takaici raheela suka lullube shi cikin sark'ewa halshe yace raheela ni fa mijinki ne ta yaya za ki zab'i hanyar 'kuntata min ki hanani hake na da yarataya a wuyanki"? Zuciyata tabani cewa kina sona raheela saidai akwai abunda yake dawainiya da ke yake tasiri akanki ni kuma daga yau na hak'ura da ke Ras-ras gaban raheela yafad'i sakamako batasan me wannan magana ta Amar take nufi ba tasoma nadama abunda ta aikata ta sada kai k'asa tana kuka Amar yad'ago fuskarta yace _I'm so sorry raheela bazan k'araba tun da bakyaso kidaina kuka kinji_ Tsanani son had'e sonshi suka chakuikuiye mata zuciya har ta bud'e baki tabashi hank'uri yarigata ta hanyar d'ora yatsaya shi a _lips_ d'inta yace shhh _wipe your tears please I will never repeated again okay_ Yana gama fad'ar haka yafice daga d'akin yana rufe _buttons_ d'in rigarsa raheela tabishi da kallon tausayi mai cike da tsatsan son tana gani yafita ta kifa kanta a _pillow_ tana kuka mai tsunma zuciya. Amar yana fita yanufi _bedroom_ d'insa ya yi zaune a gefen gado yana zance zuci tabbas sai na nunawa raheela cewa ni cikakke namiji ne bana cikin mazan da mata suke gara Kansu zan yi k'ok'ari na danne duk wani abu da nakeji akanta tun da na fahimce a yanzu tana sona zan jira har sai kin kawo kanki gareni yayi wani mushiriki murmushi yashige _bathroom_ ...... Jeeddah Aliyu🌹 [11/08 9:42 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [11/08 8:14 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 1⃣0⃣3⃣ Tun daga ranar Amar yadaina kula raheela duk lokacin da tayi girki yana zama ya narki abinsa, in kuma yafita _office_ da yadawo zai sake wanka yafita ba zai dawo gida ba sai tsakiyar dare a lokacin zai zauna yacika cikinsa, da gari Allah ya waye zai sake fita sai kuma yamma zai dawo gaba d'aya yakauracewa zaman gida tsawon sati d'aya cur kenan raheela tarasa gane alk'ila da Amar yadosa, tuni tayi nadama had'e danasani ga tsanani son Amar da yake dawainiya da ita tarasa hanya da za tabi domin tabashi hank'uri. Raheela na zaune a falon ta zabga, d'an uban tagumi duk ta rame tayi 'kashin wuya abin duniya yataro ya yi mata yawa ta kuma rasa tudun dafawa ta mik'e tana tangad'i kamar 'yar maye tsabar yunwa ce kuwa ke cinta tanufi _bedroom_d'inta har tacire kayanta tayi wanka ta tuna _pad_{auduga} d'inta tak'are da yake tana _period_{fashin sallah} Ta ja tsoki mtss tasaka dogon hijab d'inta tafita kaitsaye ta nufi, _main gate_ tun kafi tak'arasa tafara kwadawa _Joseph_ kira da gudu yak'araso wurinta, ta mik'a masa _N1000_ ta kuma fad'a masa abunda zai siyo mata tajuya cikin gida yayinda _Joseph_ yanufi inda ta aike sa. Tayi zaune a _parlour_ tana jiran _Joseph_ yadawo daga aike da tayi masa. Dr Amar matawalle ke ta danna _horn_ a gate d'in gidansa amma shiru _Joseph_ bai fito ya bud'e masa gate ba Amar ya harzuk'a matuk'a cike da bacin rai yafito ya bud'ewa kanshi daga bisani yashiga da mota yana gama _parking_ yafito daga cikin mota yana rataye da _briefcase_ a kafad'arsa hannu sa d'aya na rik'e da _coat_ yanufi cikin gida kafin yak'arasa shiga ya hango _Joseph_ yashigo hannu shi rik'e da Leda Amar yaja yayi tsaye yana aika masa, da sak'on harara tambaya ta farko da Amar yafara aika masa daga ina kifito"? _Joseph yafara magana cikin gurbataciya hausa shi da ta zame masa kamar dole Madam ne ya aike mu siye wannan_ ya nunawa Amar Leda Amar yakar6i ledar yace _okay Go back to your work_ _yes sir Joseph yafad'a had'e da juyawa_ Amar bud'e Leda idanu shi sauka bisa _ultra_{pad} take yaji wani irin bacin rai had'e da kishi ya lullube shi cikin zafi rai yak'arasa shiga gida tana zaune a _parlour_ tana fama da tunani sa da ke neman yakasara mata zuciya, cikin hargowa yace _how dare you raheela I think you are insane_ A tsorace ta mik'e tsaye domin kamar saukar aradu taji saukar muryar sa a kunnenta, cikin rawar murya tace laifi me nayi yaa Amar"? Ke wace irin sakarai ce"?shine don tsabar iskanci za ki aike _Joseph_ siye _ultra_ don ki nuna masa kina _period_ koh"? Raheela ta girgiza kai Amar ya ja tsoki had'e da jefa mata ledan akan fuska, ya haura _upstairs_ har yana had'awa da gudu raheela tabishi da kallo daga bisani tad'auki Ledarta da kuma chanji ta da yafad'o daga cikin leda tanufi d'akinta tana wanka wani tunani yafad'o mata da sauri tagama wanka tafito batare da tasaka kaya ba daga ita sai _towel_ tasaka hijab d'in da tacire tanufi d'akin Amar gabanta na fad'uwa saboda batasan yadda zai k'ar6i al'amari ba.... [11/08 9:06 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 1⃣0⃣4⃣ Batare da tayi _knocking _ ba ta murd'a _handle_ tashiga d'akin dai-dai lokacin da Amar yafito _nicked_ daga _bedroom_{ dama yasaba da shegantaka sa fitowa daga wanka tsirara lol} Raheela ta tsinkayi k'ato tsaye zigidir idanu ta suka firfito kamar za su fad'o kasa ta kwatsama ihu had'e da cewa _wayyo Allah na shiga uku jama'a ku kawo mini d'auki nayi bak'in gani_ Da sauri Amar yajayo _curtain_{la6ule} yakare jikinsa, ya zaro idanu yace don gidanku kifita min daga d'aki, _I say get out of my room be for I deal with you stupid girl_ Da gudu raheela ta bud'e k'ofa tana shiga d'akinta ta Murza _key_ tafad'a kan gado tace cab Amma wallahi Hero ba k'aramin tantiri bane Allah ya taimake ni da yau na makace, haka raheela ta dinga zance zuci. ```WASHE GARI``` Da misali k'arfe 10:11am na safe raheela ta shirya zuwa _school_ da yake yau _lecture_ d'in safe takeda a tsatsaye tasha _tea_ tafice tana fita ta tsinkaye Amar a _parking space_ yana waya yana sanye da _black colour suit_ yasaka _sky blue shirt_ had'e da _necktie_ shima _sky blue colour_ idanu sa na manne da farin gilashi cikin zuciya raheela tace kutt amma _guy_ nan ya yi kyau kamar na bashi _lipstick_ ya tsotsa, har tak'araso yana waya don tsabar kwarewa da iya d'aukar magana irin na raheela sai tafara tsokanarsa ta hanyar rare wak'a _Ku gayama iyalin mai malfa a dare jiya mu k'are musu kallo a zigidir_ da sauri Amar yajuya yana kallonta domin ya tanbata da shi take tana k'arasa wak'arta tashige mota tafisge ta da k'arfi tanufi _gate_ Joseph ya bud'e mata gate Amar ya yi murmushi daga bisani yashiga mota yanufi _hospital_ Bayan sun fito daga _lecture_ suna tsaye a jikin mota Ayshat ta dube raheela tace _besty_ akwai abunda yake damuki da ki ke 6oyewa, raheela tasaki ajiyar zuciya cikin rauni zuciya tace _I'm in love besty I'm badly in love with him_ Ayshat ta zaro ido tsawon dak'k'a uku ta d'auka tana kallon raheela daga bisani ta kyakyale da dariyar, shak'iyaci har da su fad'uwa k'asa Raheela tayi shiru tana kallon Ayshat sai da Ayshat tayi dariya mai isasarta ta mik'e tsaye tana, kad'e jikinta tace raheela ke kuwa gari yaya kika yi sake har son Dr Amar yasami muhalli a zuciyarki"? Hmm..besty nima bansaniba _on expect_ na ji ni tsundun a cikin zazzafar soyayya yaa Amar nan take ta zaiyano mata abunda yake faruwa a tsakani su, kafin Ayshat ta furta abunda take so furtawa _phone d'in raheela ya yi ringing dama yana rik'e da hannuta gani sunan Wanda yakirata yasa ta kurma ihun farin ciki had'e da cewa shine, wallahi shine_ Ayshat tace waye"? Yaa Amar ne yakirani To kiyi _picking_ mana kin tsaya kina shirme da sauri raheela tayi _received_ cikin rawar murya tace _he..llo_ ta bangare Amar da ke zaune a _office_ d'insa yace raheela nasan kin gama lecture in baki wuce gida ba ki biyo _hospital_ kiyi _picking_ d'ina Tsanani farin ciki ya baiyana akan fuskar raheela tace me yasami motar ka ne"? Kaitsaye yabata amsa ta hanyar cewa kb yafita da ita. Okay ganina zuwa batare da yace komai ba ya yi _disconnect_ raheela yes had'e da tsalle a tsatsaye tafad'awa Ayshat dalilin kiran Amar, tafisge mota da k'arfi ta dagawa Ayshat hannu had'e da cewa sai besty za mu k'arasa magana Ayshat ta yi murmushi. Amar da ke zaune yana jiran zuwa raheela yaji an bud'e k'ofa yad'ago _sexy eye's_ d'insa ya dube k'ofa Ramlat ya gani sanye cikin matsatsu _English wear's_ sunyi masifar baiyana tsiranci ta{in mai karatu bai manta ba ramlat 'yar k'anwa umma hajara ce kuma tare suka zo office d'in Amar da marigayiya na'eema a lokacin da tayi amfani da asirtace turare da boka duguzuu yabata} Amar ya murtuk'e fuska matuk'a ya mik'e tsaye yadaka mata tsawa, yace uban me kika zo yi a _office_ d'ina"? bana yi miki gargadi akan kidaina zuwa _office_ d'ina. Ramlat ta yi wani mushiriki murmushi cikin tsabar kwarewa da sani bariki tace kayi hankuri _Dr_ zuciyata takasa amincewa da gargadi ka, ina sonka Dr Amar kamar yadda nasha fad'a maka ashirye nake da mallaka maka duk abunda kakeso daga ciki har da jikina. Mtss.. Ya ja tsoki ya d'auki _briefcase_ d'insa ya rataye ya yi mata kallon wulak'anci da tsana yace in kinga dama kifito _messenger_ yarufe mini office in kuma baki gaji da zama ba ga wurinan ki zauna, da sauri ramlat tasha gabansa tayi masa mahaukaciya runguma dai-dai lokacin da raheela ta bud'e k'ofa....... Jeeddah Aliyu🌹 [13/08 9:22 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [13/08 12:31 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 1⃣0⃣5⃣ Saura kiris tayi bakwana da numfashinta da kyar tasamu ta tattaro jarumta ta, ta kuma had'a da k'arfi hali ta dai-daita natsuwarta karaf ta had'a ido da Amar da yake Amar shima kwarare d'an duniya ne yana gani raheela sai ya rungume Ramlat tsamn yana wani sauke numfashi, yayinda Ramlat take k'ok'ari ta had'e bakinta da nashi Amar yak'i bata wannan dama gani haka yasa ta Zura halshenta a kunnenshi tafara tsotsa, kamar mayya raheela ta runtsi ido hawaye suka tsatsafo mata tasaki k'ofar ta falla da gudu duk wannnan waina da ake toyawa Ramlat batasaniba, raheela na fita Amar yaficike Ramlat daga jikinsa ya ware yatsu sa guda biyar da Allah {s w t} ya albarkace shi da su ya sauke su akan kumatu Ramlat saida ji da gani ta ya d'auke na wancan gadin, kafin tadawo da natsuwarta yakara kwasheta da wani mari, tsanani zafin mari ya ratsa kwakwalwa ta batasan lokacin da tayi zaman 'yan bori ba duwawuta suka dak'i _tiles_ Amar ya durk'usa gabanta ya nanuta da yatsa yasoma karanta mata gargadi mai cike da kaukausar murya wannan shine kashid'i na karshe da zanyi miki karki kuskure ki sake tak'o wannan k'afa naki mai kama da k'afar sauro _office_ d'ina sai na k'arya ki kuma na k'arya banza _Co's_ ke karuwa ce bakida daraja da martaba sai ki kiyaye, yana k'arasa magana yafice daga _office_ cikin zafin rai yace wa _messenger_ kai kafito da 'yar iska da ke ciki karufe min _office_ Raheela na k'arasawa wurin mota takifa kanta a jikin mota tafashe da kuka nan take, tasoma danasani zuwa _office_ d'in Amar dama abunda yakeso yanuna min shiyasa ya kirani wani irin zazzafa kishi ya turnuk'e zuciyata miyasa yaa Amar za ka yi min haka"? Da kasan yadda nake shauk'i da haukan sonka da ba ka baiwa karuwa damar shiga rayuwarka ba. Tun daga nesa Amar ya hango ta tsaye jikin mota tana kuka, yasaki murmushi jin dad'i yana karasawa daf da ita yadaka mata razananiya tsawa !ke dallah wuce mu tafi kin wani tsaya kina kuka duk Wanda yabiyo yana kallon ki iya _Romance_ idanu ki suka gani da wuce hakan watakila hauka za kiyi mtss ya ja tsoki raheela ta d'ago kod'ad'i idanu ta ta tsorawa Amar ido a lokacin d'aya sonshi da haushinsa suka baibaye ta Cikin zafin rai ta jefa masa _keys_ cikin rashin damuwa ya duk'a 'kasa yad'auka dole raheela ta bud'e mota tashiga, ya ja mota sai wani tauna _chewing gum_ yakeyi yana kad'a kai da alama duniya tayi masa dad'i, raheela na ta fama sheshshek'ar kuka cikin rawar murya tace miyasa yaa Amar ka zab'i wannan hanya don ka hutani"? Nasan na k'untata maka amma ban cancanci irin wannan mumuna hukunci, daga gareka ba,ka yi hak'uri yaa Amar kayafe mini zuciyata ba zata iya juri ganika kana tarayya da wata 'ya mace karka manta yaa Amar kai da bakinka kace ka mallaka mini zuciyarka kyauta to miyasa a yanzu za ka shigo, da wata kuchaka karuwa a cikinta"? Wani mugun kallo ya watsa mata yace Karki sake ki k'ara kira Ramlat da kalma karuwa domin itace take de6e min kewa take bani abunda nakeso mai sanyini cikin nishad'i a duk lokacin ke kika munana min, yana k'arasa magana dai-dai lokacin da suka iso gida da k'arfi ya balle k'ofar mota yafita yayinda raheela ta Mara masa baya tana rusa kuka. Amar yana shiga _parlour_ ya kishingid'e yad'aura k'afa d'aya bisa d'aya a rikice raheela tashigo _parlour_ ta zube gabansa tace hak'ik'a na tafka kuskure a rayuwata, amma a yanzu nagane gaskiya yaa Amar Dan Allah karka juyan bayan a lokacin da zuciya had'e da gangar jikina suke tsanani buk'atarka , ko kallonta Amar bai yi ba sai faman tauna _chewing gum_ d'insa yakeyi. Raheela ta shak'i dogon numfashi tamkar ranta zai fita saboda tsanani kukan da takeyi gaba d'aya duniya tayi mata k'unci ga wani masifafe son Amar da ya yi nasara dabaibaye zuciyata tace Yaa Amar Dan Allah kayi magana wannan shiru naka yana cutarda ni d'agowa ya yi cikin kwanciya hankali babu wata alama da ke nuna yadamu da kukanta yace.... [13/08 2:16 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 1⃣0⃣6⃣ Yaushe kika fara son ```mijin 'yar uwa ki``` ?? Ko kin manta da farucin da kika sha furta mini, na tsane ka bana sonka banta6a tsanar wata halitta irin ka yaa Amar kuma har abada ba zan ta6a sonka ko ba haka kike, furta min ba"? Shine yanzu don tsabar samu wuri za ki zo kina wani rera kukan munafuci ki ce wai, kina sona dayake kin d'auke ni shashasha bansan abunda nakeyi ba. in za ki daina wannan kuka kidaina domin a yadda nakeji dad'i soyayya da ramlat take bani abunda ke bakya bani banga dalili da zai sauya mini ra'ayina akanta. A da nace na tsane ka amma a yanzu ina tsanani so da kaunar ka yaa Amar wallahi nayi nadama nagane kuskure na, a shirye nake da na gyara duk wani kuskure da na tafka. Mtss..Amar ya ja tsoki yace kidaina yaudara kanki raheela, domin har yanzu ban amince, kina sona don haka ki d'age ki jajirce ki nuna mini da gaske d'in kina sona yana k'arasa zance sa ya yi tafiyarsa yabar raheela tana kukan nadama. ```kaduna``` Umma hajara da aunty asabe zaune a _bedroom_ d'in umma sai fama tubka da warwara sukeyi, aunty asabe ce take magana wai miye dalilin ki nafasa zuwa _Enugu_ bayan nafad'a miki bokanan aikinsa kamar yanka wuka ne, karki yi wasa da damarki hajara yanzu ne kike da damar d'aukar famsa wulaqanci da akayi miki a gidanan. Saida umma hajara ta shak'i ta fuzar cikin tafarfasa zuciya tace kamar yadda nafad'a miki aunty asabe nafasa wannan tafiya domin, batada amfani agareni na nemowa kaina mafita wance tafi zuwa wurin boka mafitar kuwa ita ce nayi magana da shamsu ya debo 'yan fashi su shigo gidanan su yashe duk wata dukiya da ke gidanan tass daga karshe su kashe kowa hatta da maigadin gidanan kar su barshi da numfashi duk abunda suka d'ebo dangin dukiya mu yi muraba wato {50-50} wannan shi, kadai zai sa na huce duk wani bak'in ciki da mutane gidanan suka d'auki tsawon lokacin suna gumami. Aunty asabe ta sauke gwaron numfashi tace cab wani kaya sai amale, jaki ba za iya ba umma hajara tayi murmushi had'e da cewa waye shi don ubanshi aunty asabe tace amma kuwa hajara ke bala'e ce karo da ke ba dad'i kin zo da shawara mai kyau mai cike da zalla amfani to amma kuma wani hanzari ba gudu ba ya za kiyi da Amar da raheela"? Wani kafiri murmushi umma hajara tasaki tace wad'anan ae k'anana kwari ne tafiya ta musanmman zanyi musu zuwa Enugu so nake boka ya haddasa fitina a tsani su wance zai sanya Amar yadankarawa raheela saki har uku domin na huce takaici sanadi igiya aure na d'aya da ta tsinka, daga bisani na had'a ta da shamsu ya yi mata yanka rago kinga shikenan na share babi wannan zuri'a daga doron k'asa. Aunty asabe ta kyalkyale da dariya had'e da cewa hajara bakida imani kece kika biyo halin lami sak na rashin imani da tausayi amma kuma kina nufi su shamsu su shigo gidanan su kashe kowa ban da ke wannan ae b'atata dabara ce dole a zargi da sa hannu ki a kisansu in ke mahaukaciya jahila ce 'yan sanda{police} ba jahilai bane dukan bala'i za suyi miki har sai kin fad'a da bakinki ke ki kayi sanadiya mutuwar su. Umma hajara ta kyalkyale da dariya tace tun farko yakamata ki yi min wannan tambaya amma duk da haka zan baki amsa, a yadda na tsara a yau d'inan zan fad'awa alhaji gobe zan tafi katsina biki bayan na tafi katsina sai su shamsu su aiwatarda aiki dama fad'uwa ta zo dai-dai da zama ana bikin aure Yusuf d'an gwaggo mairo, ko da bincike yafad'o kaina abin a bayaine yake kowa yasan ina katsina wurin biki tana k'arasa magana suka kyalkyale da dariyar mugunta. ```waye shamsu ``` ?? Shamsu k'ane umma hajara ne wanda ake yiwa lak'abi da killer tantiri d'an iska ne a dangin kayan maye ba abunda baya sha kuma ba Wanda baya siyarwa{drugs duller} rik'ak'e D'an fashi ne kisa a wurinshi ba komai bace tun yana aji uku a _secondary school_ aka koreshi sobda yanda gagari _teacher's_ daga lokacin yace lokaci yayi da zai fara cin gashin kanshi yafad'a wata hatsabibiya kungiya ta 'yan daba daga nan yayi fice had'e da k'auri suna har zarginshi mutane keyi akan shine ya b'anbakawa iyayye shi wuta suka mutu domin a dare rana yayi fad'a da mahaifisa har yana kirari cewa giwa tayi kusan fad'uwa su sha gara. ```A Bedroom d'in umma hajara ``` A bedroom d'in umma hajara kuwa sai faman zuba sukeyi, duk wani sharri da take yunk'uri k'ulawa sai da ta baiyanawa asabe tun lokacin da umma hajara tasaki bakinta mai kama da gugar tsunma tana zuba Alhaji Abdullah matawalle yake la6e yana sauraro duk abunda suke fad'a da sauri yafito daga ma6oyarsa, yanufi waje da sauri har yana tuntube yana fita yaciro waya ya yi magana ta tsawon mintuna biyar daga bisani yanufi _part_ d'in Alhaji Muhammad matawalle bayan shigarsa da kamar mintuna uku sai gashi sun fito tare, sukayi tsaye cirk'o-cirk'o suna kallon _main gate_ tsawon mintuna shidda zuwa takwas suka d'auka a tsaye, daga bisani 'yan sanda{police} guda biyar uku maza biyu mata suka baiyana a k'ofar gidan maigadi yabud'e masu k'ofa suka shigo....... Jeeddah Aliyu🌹 [13/08 9:23 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [13/08 8:04 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 1⃣0⃣7⃣ Da hanzari Daddy da Abba suka nufi wurin su yayin da Abba yak'ara yi wa _inspector salis_ bayani irin ta'addaci da kunne sa suka jiyo masa ke umma na k'ulawa kaitsaye Abba yajagoranci _police_ d'in zuwa d'akin umma hajara har yanzu suna nan zaune inda suke zaune tun farko, motsin bud'e k'ofa yasa sukayi shiru domin jiran mai shigowa Abba yace _inspector_ bissimallah ga sunan kutafi da su Ku tuhume su da tuhama da laifin kisan kai a razane umma hajara da aunty asabe suka mik'e tsaye kowane su da yanayi tashin hankalinsa cikin sark'ewa murya umma hajara tace lafiya Abdullah su waye za'a tuhuma da laifi kisan kai"? In kinje _police station_ su za su amsa miki tambayoyo ki nan take inspector salis yaciro ankwa{handcuffs} yabugawa umma hajara da aunty asabe gani haka yasa suka fara ihu da gurnani kuka mai matukar k'aran gaske har _neighbour's_ ana jin sautin ihu da kururuwa su sanadi da yasa aunty amarya tafito domin gani abunda ke faruwa, aka iza k'eyarsu gaba mami na d'akin kwance taji ihu yakarad'e gidansu da gudu tafito, tana fitowa taci karo da umma hajara da aunty asabe cikin ankwa{handcuffs} tasoma tasalima da tambayar, meke faruwa, kafin tasami amsar tambayarta kaka tak'araso tana fad'ar yau kuma wace masifa ce hajara kika d'auko har da su jami'ai tsaro a ciki"? Yayin da _police_ ba su tsaya sauraro amsa da umma hajara za ta bayar ba suka jefa su mota had'e da yin awon gaba da su gaba d'aya mutane unguwar suka fito suna kallonsu. Sai lokacin Daddy da Abba suka k'orawa mutane gidan bayani ae kuwa kaka ta hau bakinta,inda take Shiga ba nan take fita ba{su kaka an tsallake rijiya da baya}. ```Abuja``` Raheela tana gani Amar yatafi yabarta, ta mik'e da kyar tashiga, d'akinta ta zube bisa gado tana kukan rashin mafita had'e da danasani daga bisani tashiga _bathroom_ ta tsalla wanka tafito batare da tayi _make up_ ba tasaka 'yar k'arama riga iya guiwata ta tsaya kanta ba d'an kwali tanufi _parlour_ Amar yana zaune hannushi, rik'e da _remote control_ yana chanza _channels_ cikin 'yar siririya murya tayi sallama, kallon d'aya Amar ya yi mata ya kauda fuska, ya amsa mata sallama adaki'le duk da haka raheela batayi k'asa da guiwa ba tanufi wajenshi ta durk'usa gabanshi, tafara magana cikin rauni murya duk d'an Adam baya wuce kuskure a rayuwa sa nasan nayi kuskure a baya a yanzu ina da muradin na gyara miyasa yaa Amar ba za ka bani dama gyarawa"? musanmman yanzu da ka fahimce cewa na kai k'ololuwa a sonka ka tausaya wa zuciyata _hero_ wallahi ina tsanani sonka a shirye na da na zauna da kai yaa Amar kuma nadaina kallonka a matsayin```mijin 'yar uwa taa``` Kallon banza ya watsa mata ya yatsine fuska daga bisani ya kauda fuska cikin sanyi jikin raheela ta mik'e tanufi k'ofar fita zuciyrata na tafarfasa kamar daga sama taji sautin murya sa yana rera wak'ar _2face_ mai take _if love is a crime_ da sauri raheela tajuyo cikin zuciyata tace lallai hero yashirya rama duk wulaqanci da nayi masa idanu ta suka ciko da hawaye tafita da gudu, yayin da Amar ya ji tausayinta yamashi da sauri ya mik'e ya Mara mata baya har yarik'e _handle_ ya bud'e k'ofar d'akinta sai kuma yafasa ko me yatuna !oho. ```WASHE GARI``` Raheela ta tashi da zazzafa ciwon kai amma haka nan ta shirya zuwa school saboda tanaso gani Ayshat tabata shawara yadda za ta shawo kan matsala da ke tsakaninta da Amar. Wani mugun kallo Ayshat ta watsawa raheela daga bisani, tace duk laifi ki ne raheela ta yaya kina son mutum sannan ki kasa bashi kanki wannan ba so bane ina tsanmani har yanzu da sauran tsanar Dr Amar a zuciyarki, da sauri raheela ta girgiza kanta had'e da cewa wallahi _besty_ ina matuk'ar son yaa Amar kuma a shirye nake da na bashi kaina ni dai muradina yadaina kula wannan 'yar iska. Ayshat tasuke ajiyar Zuciya daga bisani tace za ki amince da duk abunda nace kiyi za kiyi komai wuyarsa"? A yadda nakeso Hero Ayshat duk abunda kikace nayi zanyi muddin bai sa6awa addina ba. Tsawon lokacin Ayshat tad'auka tana d'orawa raheela lacca nan take raheela ta hadace ta kuma k'udiri aniya, yiwa Hero d'inta da wannan shawara raheela tanufi gida cike da zumudi yau za ta shayarda Hero _lipstick_ har sai yace yagaji..... [13/08 9:20 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 1⃣0⃣8⃣ Tana isa gida _handbag_ d'inta had'e da tarin _handouts_ ta ajiye d'akin tanufi _kitchen_ Kusan abinci kala uku ta girkawa _Hero_ kuma duka _favourite_ d'insa tasan dole ya yaba, tana kamalla girki ta jera a _darning table_ ta nufi _parlour_ tasake gyara shi ta jona _burner_ a socket ta zuba turare wuta d'an Maiduguri gida yad'auki k'amshi yau kam raheela tafito amarya sak daga bisani tanufi _bathroom_ ta cika _bathtub_ da ruwa masu d'an d'umi-d'umi ta zuba _bubbles bath_ mai 'kamshi gaske ta cire _towel_ d'in jikinta tafad'a ciki tana wanka tana hango kanta ita da yaa Amar suna tafka soyayya ta fitar hankali, tana gama wanka tafito daga _bathroom_ tanufi _dressing mirror_ ta cha6a _make up_ ta kece raini wani _boos short_ tasaka _red colour_ da wata 'yar k'arama _armless top_ _yellow colour_ ayi mata Zane zuciya da red colour" iya k'irjinta kadai tarufe ta tufke gashinta da red colour d'in _ribbon_ _lips_ d'inta yasha _lipstick_ tak'arewa kanta kallo a _mirror_ tayi murmushi had'e da godewa Allah da wannan kyakyawa sura da yayi mat tad'auki turare _natural beauty_ tafesa tak'ara d'aukar _eternity woman_ tafesa saida ta fesa turare kusan kala biyar sannan ta, bude _bedside drawer_ tadauko _lollipop_ ta b'are had'e da jefawa baki a hankali ta jaye _curtain_ d'in window tana kallon bakin gate ko Allah zai sa ta hango, haske da ke haskaka zuciyarta, tsawon _ten minutes_ ta d'auka a tsaye daga bisani ta ji _horn_ d'insa tasauke ajiyar zuciya har ya yi _parking_ idanuta na bisa kanshi tsanani sonshi ya ratsa zuciyarta ta lumshe idanu tana gani yashigo cikin gida tasaki _curtain_ ta zauna a gefen gado tana tunani daga ina za tafara saida ta share tsawon _12 minutes_ tana neman mafita daga bisani ta yanke shawara fita. kaitsaye _down stairs parlour_ tanufa yana zaune bisa _darning table_ yana cin abinci cikin yanga take tafiya, Amar ya shak'i k'amshi turareta ya lumshe _sexy eye's_ d'insa a yangace ta je kujera ta zauna tace sannu da zuwa Hero" Wani irin _shock_ ya ja Amar sakamako hango cinyoyi raheela a fili da yayi da kyar ya hadiye loma bakinsa cikin zuciyarshi yace wannan yarinya so take ta kashe ni ne"? Ya ajiye _spoon_ da k'arfi ya mik'e yanufi _parlour_ ya zauna raheela ta yi murmushi had'e da furta yau sai na k'ure maka maleji ta mik'e tanufi inda yake zaune ta zauna kusa da shi ya mik'a hannu yad'auki _remote control_ da sauri tad'auke _remote_ d'in tayi k'asa da murya tace _are you still angry with me_ ? Mtss ya ja tsoki had'e da kauda fuska tasaka hannuta tajuyo da _face d'inshi suna facing in juna tace I'm so sorry hero please forgive me_ Shiru ya yi tamkar mai nazari raheela tak'ara cewa _please hero I say I'm sorry_ ta ciro lollipop d'in bakinta tasaka masa a baki cikin zafi rai ya buge mata hannu, yace....... Jeeddah Aliyu🌹 [14/08 9:42 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [14/08 6:37 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 1⃣0⃣9⃣ _look_ raheela banaso damuwa ki kyaleni kinji koh"? Raheela ta marairaice murya tace, ina sonka hero duk abunda kayi burgeni kakeyi sai, naji kamar na goyoka na zagaye garinan da kai ina cewa yeee ko zo Ku ga mijina kyakyawa mai kama da ni saidai nafishi kyau tak'arasa magana had'e da yi masa gwalo. Amar yak'ara tsuke fuska{shi a dole class yake ja nace kaji da shi Tsoho d'an duniya ana so ana yanga} Yace ke wa kika fi kyau"? Kai mana ko kana shakka ne a gwada"? Me za'a gwada"? Kyau mana" Na fahimce cewa yau wani sabon iskanci kike ji, kin kuma sani sarai, zan yi miki abunda nasaba yi miki. Wani mahaukaci ihu raheela tasaka had'e da tsalle, tace yau burina ya cika na zo wa hero da sabon iskanci, da gudu tashiga _kitchen_ yayin da Amar yabita da kallon tsoro cikin zuciyarsa yace na Shiga uku me ke damu yarinya nan"? Allah yasa ba bini ki lalace tasha{tutolin} raheela ta bud'e _fridge_ ta d'auko gwagwani _Amstel Malta_ domin tasan shine _favourite drinks_ d'in Amar ta d'aukowa kanta _fanta_ tafito da d'an ihunta ta balle gwagwani ta mik'a masa had'e da cewa _let's celebrate_ mtss Amar ya ja tsoki cike da jin haushi raheela yarinya nan tanaso ta rainani amma zan yi magani ki gani yak'i k'arba yasa ta ajiye drinks d'in bisa _stool_ cikin shagwaba tace tun da ba za ka sha ba nima bazan sha ba kai ne kace kullum da Tsoho iskanci na ke zuwa maka yau na zo maka da sabo amma ka yi min wulaqanci. Amar ya cije _lips_ d'insa yana mata kallon k'asan ido daga bisani kuma ya galla mata, yace _to hell with you ke da Sabon iskanci naki_ in kika nemi ki kaini bango kinsan abunda zai biyo baya. Turo baki tayi tace kai komai akayi ba'a burgeka don ka ga ina sonka shine kake mini wulaqanci Allah sai in daina son naka. Cikin zafin rai Amar yaficiko ta tafad'o kanshi ya yi mata bak'ar matsa saida tasaki k'ara, yalala6o bakinta yahad'e da na shi ya had'e halshenta da _lollipop_ d'in bakinta yana tsotsa tamkar mayuwaci zaki, su raheela ido yaraina fata tsawon lokacin Amar yad'auko yana ya motsata saida ya tabbata yarikata mata kwakwalwa sannan yasaketa, yayin da raheela ta sulale k'asa ta zauna, tana sauke numfashi Amar ya yi murmushi mugunta, ya shafi kumatu ta yace ya akayi ne baby"? Raheela ta yi banza da shi sai faman jinya zuciya da ganga jikinta takeyi, daga bisani tayi nassara dawowa da natsuwarta tace _Hero_ _umhh_ Ina fatar yanzu ka huce? Dungure mata kai ya yi yace ban huce ba, saboda ba ki bani abunda nake mafalki mallaka ko kin fara sallah ne"? Zaro ido tayi tamkar ta ga abun tsoro umhh Hero gaskiya shishigi ka ya yi yawa ina ruwanka da sallah ta"? Murmushi ya yi yace saboda ke matata ce kinga kuwa ni nakeda ruwa da duk wani abu da yashafe ki. Sai nan da kwana goma zan fara sallah sai kafara lissafi tun daga yau. _okay_ bari nayi _checking_ da kaina zan gano ko saura kwanaki nawa na zama cikakke ango Amar yak'arasa magana had'e da saukowa k'asa yajayota ya zura hannu shi cikin _boo short_ d'inta tana gani abunda yake k'ok'ari yi yasa tasoma ihu miye haka Hero"? kai fa bakada kunya, Dan Allah ka kyaleni. Zan kyaleki amma sai kin fad'a mini saura kwana nawa na zama ango saboda nagaji raheela wallahi nagaji _I really need you in my bed_ banta6a kusantar zina ba banaso na jefa kaina mahalaka ki tausayi min raheela ki bani kanki ni kuma nayi miki alqawali zan nuna miki zalla soyayya wance ba ki ta6a mafalki samu daga gareni. raheela tayi murmushi jin dad'i ta sada Kai k'asa Amar yad'ago fuskarta, yace wallahi ina sonki raheela banta6a son wata 'ya mace sai akanki kece farin cikina burina da ace narasaki raheela da tabbas nayi ban kwana da kwanciya hankalina ki tausayawa masoyinki mai tsanani so da kaunarki. Raheela batasan lokacin da tafad'a k'irjin Amar ta k'ank'ame shi tafashe da kuka cikin murya mai cike da sautin kuka tace daina rok'o abunda yake mallaki ka Hero saboda raheela da duk wani abunda ta mallaka naka ne, na kuma yarje maka kayi yadda kaga dama da ni domin kuwa ni ta kace Hero ina tsanani sonka shiyasa nake masifar kishinka _please_ banaso ka'ra kula wannan karuwa komai kake so zanyi maka _I'll do any thing just to make you happy_ Tsan-tsan dad'i ya baibaye zuciyar Amar yad'ago fuskar raheela yasaka halshe ya lashe hawaye fuskarta tass, daga bisani yabata labari Ramlat, tsanani mamaki ne yarufeta tace yaushe Ramlat ta zama 'yar iska"? Amar ya yi murmushi had'e da cewa dama chan 'yar iska ce. to Allah ya isa ban yafe mata ba tun da ta runguma mini miji raheela tak'arasa magana har da su murgud'a baki Kyalkyalewa da dariya Yak'ara mannata a k'irjinsa, yana wani shafa gashin kanta _Raheela troublemaker_ wannan Allah, ya isa d'in har da ni ciki saboda nima na rungume ta. Ta narka masa duka a k'irji tace ni bada kai nake ba saboda kafad'a mini dalilinka na rungumarta na kuma yafe maka amma ita kan ban yafe mata ba. Amar kan sai faman kyalkyale dariya yakeyi duniya tayi masa dad'i, sai misali k'arfe _11:20_ na dare kowane su yanufi _bedroom_ d'insa bayan shigar Amar d'akinsa da kamar _5minutes_ sai gashi yafito cikin _pajamas_ sai faman zabga k'amshin yakeyi yanufi d'akin raheela da 'yar gajeriya sallama yashiga, raheela na tsaye gaban _wardrobe_ taciro rigar baccinta sai ga Hero yashigo ta baya ya rungume ta, ya yi k'asa da murya baby yaushe wannan abin zai tafi"? Ta sunkuyarda kai 'k'asa takasa cewa komai kunya tarufe ta. Cikin kunnenta yarad'a mata _just tell me Baby_ Yadda ya yi mata magana a kunne yasa tsigar jikinta tashi ita ma ,kamar mai rad'a tace _remains 2 day's_ Chak Amar ya sunkuce ta yadinga juyi da ita sai kyalkyale dariya sukeyi daga bisani ya zube bisa gado ita kuma tana bisa k'irjinshi gashin ta yarufe mata fuska hannu yasa yatattara shi ya mayar da shi baya. tsawon lokacin, suka d'auka suna shayarda junansu soyayya mai dad'i gaske ta hanyar _Romance_ daga bisani Amar ya rungume abarsa cikin shagwa6a raheela tayi magana ta hanyar cewa hero bansaka _sleeping dress ba_ Amar yak'ara k'ank'anme ta yace nafisonki a haka baby kema za ki fi jin dad'i bacci... _asuba tagari lovebirds_ Jeeddah Aliyu🌹 [14/08 7:53 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 1⃣1⃣0⃣ ```washe gari ``` Raheela na _kitchen_ tana had'a _breakfast_ ta duk'ufa da aikin da takeyi Amar yashigo _kitchen_ d'in raheela tajuya tana murmushi tace _Good morning Hero_" Ya mayar mata da matarni murmushinta had'e da cewa _Morning baby" kintashi lafiya?_ Lafiya qalau _suit_ d'inan sunyi matuk'ar dacewa da kai kayi kyau' Na gode babynaa tsaye ya yi yana kallo raheela har tagama abunda takeyi ya tayata ta jera abinci bisa _dining table_ daga bisani tace _10 minutes_ zan saka kayana nadawo mu yi _breakfast_ Amar ya girgiza kai yace mu je na rakaki raheela ta yi murmushi, ta wuce gaba yana biye da ita _simple make up_ tasaka atamfar _Holland_ ta kwashe tarkace takardu ta tajuya wurin Amar da ke ta aikin kallonta kamar zai cinyeta, tasaki masa sanyaye murmushi, tace sorry my hero na barka kana jira. Amar yasaki ajiyar zuciya ya mik'e tsaye yace, _never mind dear_ mu je ko raheela tajuya suka five daga d'akin taja masa kujera ya zauna tayi _sarvin_ d'inshi. Amar yace kinyi min kyau raheela har naji kishi yakama ni saboda banaso mazan da ke waje su kalla mini ke. murmushi ta yi tace Hero kenan ko sun kalleni sunyi a banza saboda ni taka ce, Dad'i Yakama Amar sai wani rausaya kai yakeyi suna kamalla _break_ suka jera a tare kaitsaye _parking space_ suka nufa, kowane yanufi motarsa raheela ta kasa shiga mota tayi tsaye tana kallon Amar shima ita yake kallo sai kace yau suka fara gani juna yayin da kowane da abunda yake sak'awa Amar yakasa jurewa yanufi wurinta da sauri yabata _hot hug_ yace ina sonki raheela har banaso abunda zai sa na nisanta da ke' Nima haka Hero dai-dai da _second_ d'aya Banaji dad'i in bana tare da kai sai naji kamar ruhina baya tare da ni Kaine bugun zuciyata hero Dan Allah ka kula min da kanka. Amar yasaketa had'e da bata _hot kisses_ yace _you too baby take care of you self_ Da kyar suka rabu kowane zuciyarsa cike da kewar d'an uwa shi. ```Kaduna``` Kwana su umma hajara d'aya a hannu jami'an tsaro{police} duk sun fita haiyaci su, a washe gari 'yan sanda{police} sukayi nasara chafko shamsu killer a lokacin da Daddy da Abba suka iso police station su umma hajara an sha jinga 'yan sanda duk sun farfasa mata baki yanayi kamanu da halitta ta sun sauya saboda tsanani dukan da tasha, aka fito da su tana gani su Abba tafara kuka had'e da rok'on gafara Abba ya watsa mata kallon, tsana daga bisani yaciro farar takarda ya cilla mata yace wannan takarda dana cilla miki bata buk'atar dogon bayani domin kin fahimce abunda take nufi dama saura igiya biyu a yanzu kuma na tsintsinka su gaba d'aya, umma hajara ta kurma ihu kamar sabon kamu hauka ta rik'o k'afar Abba tana gunji kuka Abba ya han6areta yayin da mijin aunty asabe yana gefe yana jiran Abba ya gama nasa aiki shima ya aiwatar da nashi, aunty asabe nagani mijinta tace wallahi sharri sukayi min babu hannuna cikin wannan chakwakiyar, cikin zafi rai alhaji bukar yace ki je nima nasake ki saki uku kuma ko lahira bana fatar Allah ya had'ani da ke daga haka yajuya yafice yayin da kukan hajara da asabe yakarad'e _police station_ Daddy da Abba suma sukayi tafiyarsu dama hausawa sunce k'arshen alawa k'asa. ```ABUJA``` yau raheela ta tashi da matsananci fad'uwa gaba saboda yau ne tafaara sallah, ta kuma San hero ba d'aga mata k'afa zai yi ba dole yau ya k'arbi abunda ya jima yana mafalki mallaka ga shi raheela ta ca6a ado cikin wata rikitaciya rigar bacci _pink colour_ bakinta yasha _lipstick_ saboda tasan abunda Hero yafiso kenan, lungu da sak'o na jikinta yana fitarda fitinane k'amshi saidai kash zullumi had'e da tsoro sun hanawa raheela cika alqawali da tad'aukawa Hero na kai masa kanta, har _bedroom d'insa_ cikin zuciyata tace naga takaina ni raheela ya zanyi da Hero"? [14/08 9:45 pm] Jeeddah Aliyu🌹: [14/08 8:44 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 1⃣1⃣1⃣ Tsawon lokacin raheela ta share a zaune tana, nenan fita _ringing_ d'in wayarta yadawo da ita daga natsuwarta, ras gabanta yafad'i sakamako gani suna Hero na yawo akan screen d'in wayarta jikinta na rawa tayi picking a tsorace tace, _Hello_ Amar da ke kwance bisa k'aton gadonsa yana jira tsanmani, ya wani lumshe ido yace _Hi baby kina kallon agogo kuwa?_ Wata katuwar ajiyar zuciya raheela tasaki had'e da kallon agogon bango d'akin _11:2 na dare_ _Baby karki sa6a alqawali kinji_ Da kyar raheela ta bud'e baki hawaye na zuba daga idanu ta tace tsoro nakeji bazan iya ba Hero. Haba baby Ashe duk son da kike kirari kina min k'arya ne har yanzu da ragowa kiyayyata a zuciyarki. _No Hero wallahi ina sonka kawai dai ina jin tsoro ne_ Shikenan ki zo ki tayani kwana ba abunda zanyi miki kinji"? Da sauri raheela tace da gaske Hero ba ka za yi min komai ba"? Kwarai kuwa babynaa ba abunda zanyi miki _okay_ Raheela tafad'a had'e da mik'ewa ta d'aura zani bisa rigar baccinta ta suri _slippers_ d'inta tanufi _room_ d'in Amar cikin 'yar siririyar murya tayi sallama Amar ya amsa mata ya mik'e daga kwance yanufi wurinta yace baby kinada alwala"? Raheela taga kai hijab Amar ya mik'a mata cikin sanyi jikin tasaka yajagorance su sallah raka'a biyu yadinga kwararo addu'a raheela na amsawa da _Ameen_ daga bisani suka shafa addu'ar Amar ya mik'e had'e da mik'arda ita tsaye yacira mata hijab da zani jikinta, ya wani zaro ido had'e da cewa _wow amazing you look so sexy baby_ Raheela ta sunkuyar da kai k'asa jikinta na Mazari kamar maijin sanyi, cikin rashin damuwa da halin da take ciki Amar yarik'o hannuta yanufi wata 'yar k'arama _center carpet_ mai _shape_ d'in _heart_ a tsakiyar ta an rubuta _l LOVE YOU RAHEELA_ da manya harufa ya zaunar da ita yace _just a minutes_ yafice da sauri bai jima da fita ba yadawo da wani k'aton _tray_ mai tsanani kyalli da d'aukar ido anyi rafi d'insh da Leda mai kyalli ya ajiye gabanta yanufi d'an k'arami _fridge_ yadinga jido _drink's_ masu sanyi yana ajiye wa gabanta ya kashe wutar d'akin duhu ya mate d'akin daga bisani ya zauna kusa da ita ya d'auki wani d'an k'arami remote yaddana sai ga haske yana fitar da _different lights colour red, blue, yellow, pink whites & black_ sai ga wani tangameme photo su ya baiyana a jikin bango yanayi sa kamar _plasma tv_suna manne da juna sunyi masifar kyau Amar ya kira sunanta a k'asan mak'oshi _raheelaaah_ masifafe sanyi nan da takeji duk lokacin da Amar ya yi mata irin wannan kira ya lullube ta da kyar d'ago idanuta Amar yanuna mata jikin bagon d'akin inda photo su ke shawagi yana fitar da kaloli haske daban-daban...... [14/08 9:42 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 1⃣1⃣2⃣ Idanu raheela suka sauka bisa photo su ko wane colour yafito sai photo ya kuma irin colour sai kuma rubutu ya baiyana da wani colour daban an rubuta _HAPPY OUR FIRST NIGHT RAHEELA_ da manya harufa da sauri raheela ta sada kanta k'asa gabanta na cigaba da fad'uwa yayin da Amar yaye Leda da akayi rafin d'in _tray_ gasasu kaji suka baiyana akai sai k'amshi suke zuba _{ni kan 'yar gidan Shehu Aliyu na hadiye wasu masifafin yawu nace wallahi ko ta yaya sai na yagi rabona kuma har na yiwa Autar Hajiya guziri da cinya lol_} Amar yad'auki 'yar k'arama _knife_ ya yanko katuwar cinya yasakawa raheela a baki yace ci kaza baby dama nayi miki alqawali a first night d'inmu za ki ci kaza sai kin ture cike da tsoro raheela ta tasgi kazar yayin da Amar yacigaba da d'ura mata kaza sai da tace na k'oshi hero yabarta haka nan yace mu je na rakaki _bathroom_ kiyi _brush_ da kanshi ya d'auko brush had'e da _toothpaste_ mai k'amshi _strawberries_ ya matsa akan brush d'in ya mik'a mata hannu raheela na rawa ta k'ar6a duk abunda takeyi yana, tsaye ya rungume hannu a k'irji yana kallonta, tana kamalla brush ta d'auki _mouth spray_ shima mai k'amshi _strawberry_ tafesa a bakinta a sanyaya tajuya yayin da Amar ya Mara mata baya, har Amar ya wuce ta tanan tsaye a bakin k'ofar _bathroom_ Raheelaaah" Amar ya kira sunanta Raheela ta runtsi ido jin takeyi kamar ta kurma ihu _Zo nan raheela ba abunda zan yi miki kinji_ Girgiza kai tayi idanu ta na tsiyaya hawaye saboda yanzu kam ta fahimce yau Mai rabata da yaa Amar sai Allah Tsanm ya mik'e yanufe ta da sauri raheela tashige cikin _curtain_ tana kuka, yaye _curtain_ d'in yayi yad'auke ta chak yajefa ta bisa gado yayin da raheela ke ta faman girgiza kai tana ja da baya karaf idanu ta suka sauka bisa _bedsheets_ shima da Zane zuciya an rubuta _I LOVE YOU RAHEELA_ A hankali Amar ya hayo gadon cikin zafi nama ya chafko k'afar raheela yajayonta da k'arfi, yayi mata kyakyawa muhalli a k'irjinshi, nan take yalalu6o bakinta yasoma tsotsa, yanayi yana shafar lallausar fatarta, daga bisani yacire 'yar rigarta yajefa, raheela sai faman kuka takeyi abun gwani ban tausayi, _{nace Allah sarki raheela aure kenan aure yak'in mata}_ Amar kam bai fasa yunk'uri cima burinshi yakeyi, wani razanane ihu da raheela ta kurma shi ya tabbata mini da cewa _Dr Amar matawalle_ ya tsallaka _border_ sai kawai nafara jin raheela na cewa wayyo kaka Hero zai kashe ni wayyo k'afafu na Dan Allah Hero kayi hank'uri wallahi mutuwa zanyi, Saida Amar ya tabbatar da ya kashe wutar zazzafar k'aunar raheela da ke tururin a zuciyarshi sannan ya kyalleta ya wani k'ank'anme ta yana sauke numfashi, raheela kuma sai faman shasshek'ar kuka takeyi......... _I'm sorry masoyan mijin 'yar uwa taa yau naso na kawo muku k'arshen wannan labari saidai Allah bai nufa ba sai kuma gobe in Allah yanufi mu da kaiwa_ Jeeddah Aliyu🌹 [17/08 11:11 am] Jeeddah Aliyu🌹: [16/08 5:09 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 1⃣1⃣3⃣ ```WASHE GARI``` Tun da asuba Amar yad'auki raheela yakaita _bathroom_ yacika _bathtub_ da ruwa masu d'umi yasaka _dettol_ yasakata ciki wani mahaukaci ihu ta kurma ta chukuikuiye wuyan rigar Amar tana kuka, yayin da shi kuma yake aiki rarrashinta saida ruwan suka huce yak'ara saka wasu yayi mata wanka tass, sannan yafice yabarta ta tsalkake jikinta raheela tafito d'aure da _towel_ iya cinya sai wani Jan k'afafu takeyi Amar rik'o hannuta yabata zani ta d'aura yasaka mata hijab had'e da shinfid'a mata _pray mat_ tayi sallah tana kamalla sallah ta zabga tagumi, Amar yashigo d'auke da _teacup_ ya mik'a mata mai d'auke da _tea_ mai kaurin gaske a sanyaye raheela ta k'ar6i _cup d'in_ ta fara _slipping_tana yatsinar fuska ta shanye tea d'in ta ajiye cup ta kauda fuskarta gefe Amar ya yi murmushi saboda ya fahimce raheela kunyarsa takeji yad'auke ta chak ya shinfid'e ta bisa gado ya kuma cire mata hijab sai ya ji jikinta ya yi zafi alamar zazzab'i magani yabata tasha daga bisani ta kwanta, ya rufa mata _blanket_ ya sunbace goshinta sannan yafice daga d'akin, yayin da raheela ta lumshe idanu ta, hoton abunda yafaru tsakaninta da Hero daren jiya yadawo mata a kwakwalwa take tafara jin sabon sonshi yana ratsa jini jikinta tacigaba zance zuci har bacci ya yi nasara yin awon gaba da ita. ```k'arfe 11:15am``` Sai lokacin raheela ta falka, ta mik'e da kyar ta nufi d'akinta, kaitsaye _bathroom_ ta wuce tayi wanka ta zauna gaban _dressing mirror_ tayi _simple make up_ ta bude _wardrobe_ ta d'auko atamfar _super English_ _papule colour da touch's d'in orange_ tasaka tafeshe jikinta da turare masu k'amshi gaske, tana cikin d'aura d'an kwali Amar yashigo cikin tsadadiya shadda _ash colour_ gashin kansa yasha gyara sai kyalli yakeyi, ta ciki _mirror_ suka had'a ido da sauri raheela ta sada kai k'asa Amar yasaki murmushi, yak'arasa daf da ita ya rungume ta yad'aura kanshi a kafadar ta chan k'asan mak'oshi yace _Good morning my Angel_ Raheela ta rufe fuska da tafi hannuta, cikin 'yar muryata mai dad'i tace _morning Hero_ Amar yashafi wuyanta da hannu shi yace ya lafiyar jiki ina fatar babu inda yake miki ciwo"? Turo baki tayi cikin murya shagwa6a tace cinyoyi na kadai ke min ciwo kuma bana iya tafiya da kyau tausayi ta yakama yaa Amar yace _I'm sorry baby zai daina ciwo tafiyarki zai dawo normal kinji_ raheela taga kai alama ta gansu da bayani sa yarik'o hannuta suka sauk'o _downstairs_ kaitsaye _dining table_ yanufa da ita yad'auki _plate_ ya yi _serving_ da kanshi yadinga _feeding_ d'inta har ta k'oshi sannan shu kuma yacika nasa ciki daga bisani suka nufi _parlour_ a _three star_ Amar ya zauna yajayo raheela ya manna ta a k'irjinshi yayin da ita kuma talafe kamar magge. ```kaduna``` Duk yadda 'yan uwa umma hajara suka so Abba ya hak'ura yasaka baki _police_ su bada beli su Abba ya k'i amincewa da wannan, buk'ata tasu haka suka cigaba da sintiri zuwa waje Abba da Daddy daga karshe saida suka had'a Abba da dattijai da yake jin kunya had'e da ganin girmansu sannan Abba ya amince aka sake su sadai Abba yakafa sheda duk abunda yasami danginsa su ne mutane na farko da zai fara tuhuma, a bisa wannan sharad'i Abba ya amince aka bada belinsu suna fitowa daga _police station_ babban yayasu Alhaji sadi yadakata da su ta hanyar cewa ina fatar kuna da muhalli da za Ku zauna domin ni banida matsunnguni Ku a gidana hajara da asabe suka k'asa suna rok'onshi yarufa musu asiri yace iya rufin asiri da zanyi muku kenan da nayi tsaye tsayin, daka aka fito da Ku don haka Ku Kama gaba Ku, tun dare baiyi muku ba kunemi muhalli da Ku tsugune yana gama magana yaja motarshi yayi gaba duk gidan 'yan uwa da suka dosa k'ora kare akeyi musu daga karshe sai k'onane gidan mahaifisu suka nufa, a _boys Questar's_ suka zauna shima d'akuna wuri duk su rube in ana ruwan sama a tsaye suke, kwana saboda duk rufin ya farfashe a haka suke rayuwa mai cike da matsi da 'kuncin abinci da za su ci sai in 'ya'ya asabe su aiko mata ta d'an samma umma hajara tun kafin tafiya tayi nisa asabe tafara yiwa umma hajara gori tagaji da cida k'atuwa banza don haka umma hajara taje ta nemo na kanta... [16/08 6:09 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 1⃣1⃣4⃣ Tun daga ranar tadaina samma umma hajara abinci, ko taci tarage saidai ta, zubar dole umma hajara tafara fita neman aikatau kada yunwa ta halak'ata, da kyar tasami aiki wanke-wanke a bakin tasha shagon wata bayarbiya mai siyarda abinci duk Wanda yaci yarage ta zube cikin Leda a haka take samu abunda taci _dama ance in za ka Gina ramin mugunta ka Gina sa gajere watakila kai ne za ka fad'a ciki duniya ta juyawa umma hajara baya tayi danasani abunda ta aikata a rayuwata_ ```WATA UKU ``` Amar da raheela na gudanarda rayuwar su cikin so da kaunar juna, yau raheela ta tashi da zazzab'i da Amai yayin da Amar duk yarudi daga karshe ya yi mata _pregnant test_ yagano cewa tana d'auke da ciki d'an wata biyu, nan take yadinga ihu yad'auke ta chak yana juyi da ita, tun daga lokacin yak'ara bata kulawa ta musanmman cikin raheela na da wata biyar Amar ya yi mata _scanning_ yagano cewa tana d'auke da _twins_ duka maza ranar Amar har da kuka ya yi saboda farin ciki. A hankali raheela take saukowa daga _upstairs_ sai fama tura tintsitsi cikinta takeyi Amar da ke zaune a _parlour_ hannu shi rik'e da _magazine_ yana d'agowa ya hango raheela ya mik'e da sauri yanufi wurinta yarik'o hannuta ya zaunar da ita, ya shafi kumatu ta yace sannu _baby_ raheela ta ya motsa fuska, had'e da cewa Allah hero cikin nan yana min nauyi da yawa ina zauna da kyar nake iya tashi in kuma na kwanta da kyar nake iya tashi, Amar ya yi murmushi yace _oh sorry Baby_ sai next month _EDD_ ki zai cika. Raheela tamkar zai tayi kuka tace ni wallahi na matsu na haihu ni kadai nasan yadda nakeji akan ciki nan. Kafin Amar yabata amsa lamtana tafito daga _kitchen_ da plate rik'e da hannuta, tayi sallama ta mik'awa raheela _plate d'in_ da sauri raheela ta k'ar6i plate tace lamtana har d'an wake ya nuna kamar kinsan yunwa nakeji. Amar ya zaro ido yace haba lamtana banace kidaina sakawa raheela yaji da yawa a cikin abinci ba"? Da sauri raheela ta katsi masa numfashi ta hanyar cewa gaskiya Hero kacika, k'orafi da yawa d'an wanke ba yaji ya za'ayi ya yi dad'i ci Amar ya dungure mata kai yace, sai basir ya kamaki zai kiyi bayani, raheela tayi murmushi had'e da cewa da basir yana kamani da yanzu yadad'e da kamani. Cikin raheela na shiga wata tara kaka ta dinga masifa da Amar dole yadawo da raheela gida kwana ta biyu a Kaduna tashi da nak'uda, kaitsaye aka nufi _hospital_ da ita mami na kiran Amar da waya ta sanar da shi raheela tana _labour_ a lokacin yana _office_ a rikice yashiga mota yanufo garin Kaduna, tun kafin Amar ya shigo garin kaduna mami tak'ara kiranshi tayi masa kyakyawa albishir raheela ta haihu lafiya an sami _twins_ farin ciki kamar ya kashe Amar yana shigowa _hospital_ d'in yanufi _room_ d'in da take cikin tsanani farin ciki ya rungume raheela yabata _hot kisses_ kaka ta galla masa harara tace kai fa Amar bakada kunya sai lokacin Amar ya lura da mutane da ke cikin d'akin... Jeeddah Aliyu🌹 [17/08 11:12 am] Jeeddah Aliyu🌹: [16/08 7:16 pm] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 1⃣1⃣5⃣ Ya d'an Sosa kai alamar jin kunya yanufi wurin, mami da aunty amarya da ke rik'e da baby's yafara k'ar6a na hannu aunty amarya ya yi masa, kiran sallah had'e da hud'uba, daga bisani ya tsura masa ido yaga _photocopy_ d'insa sak ya sunbace kumatu shi, ya mik'awa aunty amarya mami ta mik'awa masa na hannuta, Amar ya zaro idanu kasa boye mamaki sa ya yi yace _Allahu Akbar Allah mai iko mami kamanu yara nan irin d'aya sak_ Mami tayi murmushi tace haka ne Amar kowa abunda yake fad'a kenan Amar ya yi murmushi ya yiwa yaron h'uduba kamar yadda ya yiwa d'an uwansa. ```RANAR SUNA ``` Yara suka ci sunan Daddy da Abba akayi musu lak'abi da Arman da Aryan raheela na hango tayi tasha make up tana sanye da wani tsadad'e lashi, Ayshat da zainab amarya saboda ba'a fi watani uku da aurenta da Dr kabeer sai faman hidama sukeyi da jama'ar da suka gaiyato anyi bikin suna lafiya ank'are lafiya, yayin da maijigo da yaranta suke samu kyakyawa kulawa daga wurin kaka musanmman raheela da kaka keta faman tsinma ta da had'ad'u kayan mata. Amar kuma sai faman sintiri yakeyi tsakani abuja da Kaduna sai da raheela tayi wata uku a lokacin yaranta sunyi kwari sannan kaka ta amince takoma gidan Amar ranar saida Hero ya suma don dad'i saboda raheela tadawo masa budurwa sak. ```BAYAN SHEKARA BIYAR``` Raheela ta cikawa Daddy burinsa ta zama cikkakiya likitan mata, yayin da Daddy da Abba suka ware billiyoyi kudi suka Gina katafare _hospital_ mai suna *Abdulrazaq matawalle memorial hospital* domin tunawa da mahaifin su inda Amar da raheela suka tattaro komatsa suka dawo Kaduna da zama saboda kula da hospital d'insu yayin da suka tare a tafatsitsi gidansu da yaya su guda uku saboda a lokacin raheela tak'ara haihuwa 'ya mace mai sunan na'eema suna kiranta da Ainaan burin Amar yacika ya mallaki raheela rayuwa suke gudanarwa cikin kwaciyar hankali da kaunar juna. Raheela na zaune gaban _dressing mirror_ tana make up Amar yashigo yana sanya da _English wear's_ harara ya galla Mata daga bisani yace wai ke duk lokacin da za mu fita sai kin 6atawa mutane lokacin, raheela ta yi murmushi had'e da mik'ewa tsaye ta d'auke _handbag_ da _veil_ d'inta tace mutafi sarkin k'orafi har ta juya Amar yafisgo ta da k'arfi ya tsotsa _lipstick_ d'in bakinta, sannan yasaketa raheela ta kai masa duka da _handbag_ cikin shagwaba tace haba Hero kai kenan kullum sai ka tsotsi min _lipstick_ Amar ya rungumo ta suka nufi k'ofar fita yace _sorry babynaa duk lokacin da naga lips d'inki da lipstick banida kwaciyar hankali har sai na tsotsa shi_ Raheela tayi murmushi had'e da cewa ni ma shiyasa akoda yaushe nake shafawa saboda nasan _my super Hero_ yana matuk'ar sonshi Dad'i ya lullube Amar yace ina sonki raheela kuma har abada kece taurarowa da ke haska zuciyata. Suna k'arasa shiga _parlour_ yaransu da ke zaune suna jiran fitowarsu a lokacin d'aya suka mik'e Ainaan yarinya 'yar shekara biyu tanufi wurin Amar da gudu da sauri yasake raheela yad'auketa yace _oh my angel I miss you_ Ainaan ta kyalkyale da dariya cikin 'yar muryarta ta yara tace Daddy yoyipop{lollipop} Amar yajuya ya kalli raheela suka kyalkyawa da dariya Aryan yace Daddy karka 6ata saboda ko yanzu guda, uku tashanye Amar ya yi murmushi ya shafi kan Aryan suka fice daga gidan..... [17/08 8:05 am] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 {Part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 1⃣1⃣6⃣ Raheela na _driving_ yayin da Amar ke ta faman yiwa Ainaan wasa _traffic light_ ya tsayar da su gungu almajirai suka lullube titi suna bara raheela ta bud'e _handbag_ d'inta ta Ciro _N500_ ta zuge glass da sunan tabada sadaka karaf idanu ta suka sauka bisa ga wata mata gurguwa zaune cikin keken guragu ta tsura mata ido yayin da hawaye ke fita daga idanu matar ganita ya yi masifar firgita raheela, har takasa mik'a sadaka da tayi niyar bata a dai-dai lokacin aka basu hannu cikin mutuwar jiki raheela ta ja mota cikin zuciyarta tace tabbas wannan matar tayi kama da umma hajara in har ita ce to ya akayi ta zama gurguwa"? Nan take raheela ta tuna da wasiyya da na'eema tabar mata _Dan Allah raheela kiyi mini alqawali ko bayan raina za ki kula mini da umma naa saboda batada kowa sai ni_ Ras gaban raheela yafad'i duk sanyi ac da ke cikin motar ita zufa takeyi, yayin da Amar bai San abunda ke faruwa da ita saboda ya shagala da yiwa Ainaan wasa, nan take raheela tayi yuton ta koma inda suka fito,da sauri Arman yace _mommy_ mu fasa zuwa gidan kaka ne na ga kin koma baya"? Sai lokacin Amar yad'ago kanshi ya k'urawa raheela ido ya ga tana ta faman gumi, kafin yayi magana ta gangara gefen titi tayi _parking_ tafice da sauri tanufi gungu almajirai saidai kash duk iya dube-dube raheela bataga matar ba a firgice Amar yarik'o, ta yace lafiya raheela wai me ke damuki ne"? Wallahi ita ce yaa Amar Dan Allah ka tayani nemanta na cika alqawali da na d'aukawa yaya na'eema. Amar yak'ara firgita cikin rawar murya yace wace na'eema kuma"? Cikin murya kuka raheela tabashi labari abunda tagani, da kuma alqawali da tayi wa na'eema Amar yasaki ajiyar zuciya yace daina kuka raheela insha Allah za mu nemo ta duk inda take, nan take Amar ya yi ma sauran almajirai kwatace gurguwa matar, ko sun santa sukace ta wuce gida tana kuka su ma basusan abunda take yiwa kuka kwatace gidanta su yiwa Amar, raheela tafashe da matsanaci kuka tace wallahi yaa Amar umma hajara ce ga shinan sun fad'i sunan mahaifinta, da yake daga inda suke babu nisa da gidan sai kawai suka nufi gidan suna shiga suka tararda ita a bakin ru6abe gate din gidan tana kuka asabe na bisa kanta tana zazzaga mata masifa. Ita kanta asabe ta girgiza da gani Amar da raheela, umma hajara tana gani su tak'ara fashewa da kuka tana rik'o su gafara, raheela ta d'urkusa a gaban umma hajara tace na yafe miki umma, amma ya akayi kika rasa k'afafu ki"? cikin shasshekar kuka umma hajara tafara basu labarinta, kamar yadda na fad'a muku kullum sai nafita aikatau wanke-wanke nake samu abunda naci, kamar yadda nasaba fita na nufi bakin tasha ina cikin aikina sai kawai nafara jin ihu da kururuwa maman sunday cikin shagonta,tana fitowa tarufe ni da duka wai nayi mata sata kudin duka na takeyi ta ko ina, daga k'arshe ta yi mini kuran kare batare da nasan hawa balle sauka sai faman kuka nakeyi dama almajirai da ke zama bakin shago suna jin haushina sabod in ci abinci an rage d'auka ni nake hana su na juyewa na zo da shi gida, dama irin wannan ranar suke jira ae kuwa suka rufeni da duka suna mini ihun barauniya gani za su halakani yasa na kwasa da gudu idanu na sun rufe muradina na tsirar da na raina ashe bala'i na gaba yana jirana, bansan cewa na hau kan titi ba sai jin nayi mota tayi mini kwasan karan mahaukaciya ta watsar, yayin da wata mota tabi bisa k'afafu na ni dai ban k'ara sani inda nake ba, sai tsintar kaina nayi bisa gadon asibiti koda na shafa k'afafuna sai naji su lullube cikin bandeji ashe sanadiyar take k'afafu na da mota tayi sun dameji ta yadda ba za su k'ara amfanata ba shiyasa likitoci suka gutsire su, a lokacin dangina suka k'ara nisanta ta asabe ce kadai ke jinya ta ita ma don nazami mata dole, saida na share tsawon wata uku ina jinya daga bisani aka sallame ni, ashe lokacin zan fara tsintar mumuna aikin da na aikata a baya domin sai na share kwana uku ko ruwa bansaka a bakina, da kyar nasamu yaya sadi ya siya min keke tun lokacin nafara fita bara domin ita kadai ce hanyar da tarage mini da zan iya samu abinci haka na dinga yi bara wata rana hakanan nake dawo ban samo ko kwadala ba wani lokacin kuma in asabe na ji mugunta sai kawai ta rufeni da duka tanayi tana zagina wai nice silar jefata cikin wannan hali da ta ciki rayuwa tayi mini 'kunci duniya ta juyan baya k'afafu da nake sintiri da su a gidanje bokaye da 'yan tsinbo na waye gari banida su nayi nadama abunda na aikata raheela Ku dubi girman Allah Ku yafemin ko zan samu sausauci, wannan masifar da na ke ciki umma hajara tana tak'arasa maganarta tafashe da kuka. Daga Amar har raheela sunyi matuk'ar tausaya mata, yayin da raheela tarik'o hannuta idanu ta na zubarda hawaye tace na yafemiki umma, na kuma d'auki alqawali zan iganta rayuwarki zan baki duk wata kulawa da 'ya take bawa mahaifiyarta domin na cika tsohon alqawali da na d'aukawa yaya na'eema kuka umma hajara takeyi tamkar ranta zai fita, yayin da raheela ke ta fama rarrashinta ki kwatarda hankali ki umma ina tare da ke yanzu nan zan tafi da ke zan nema miki kyakyawan muhalli kema ki rayu kamar kowa. Amar yaciro waya daga aljihu rigarsa ya kira _driver_ gidansa ya yi masa kwatance gidan da suke, bayan kamar mintuna 15 sai ga _driver_ ya zo suka kama umma hajara daga ita har keke ta suka saka su cikin mota, aunty asabe na gefe ta rakube tana kuka mai cike da nadama, raheela ta juya wurinta tace aunty asabe ki zo ki shiga mota mu tafi dama duk abunda umma hajara ta aikata da sa hannuki a yanzu ma da duniya ta juya muku baya Ku na tare don haka, umma hajara ba za ta tafi tabarki cikin wannan hali kun nufi rayuwata da ta zuri'ata da mumuna nufi ni kuma yau zan nufe Ku da kyakyawan nufi asabe ta rushe da kuka ta zube gaban raheela tana rik'o ta gafara, raheela ta kauda fuska ta tuna ada yadda aunty asabe take gudar katuwa mazaunata kadai abun kallo ne, yau tadawo 'yar firit da ita kamar mai cutar 'kanjamau duk wahala da rashin kayakyawan muhalli ya tsiyaye manya duwawu nan. Kaitsaye _Abdulrazaq matawalle memorial hospital_ driver yanufa da ita domin umarni da Dr Amar yabashi kenan sai a washe gari Dr Amar ya debi jini umma hajara akayi mata _blood test_ nan take suka gano cewa tana d'auke da cutar ciwon sugar{diabetes} shiyasa da aka yanke k'afafuta, tun daga lokacin Dr Amar shi da Dr raheela matawalle suke kula da umma hajara har tasami sauki, ranarda suka sallama ta kaitsaye wani _plat House_ mai matuk'ar kyau suka nufa da ita Amar yaciro takardu gidan ya mik'awa umma hajara yace umma wannan takardu gidanki ne da raheela ta siya miki ae kuwa, umma hajara tafashe da matsananci kuka tace kaichona yarinya da nayi yunk'uri gani bayanta yau ita ce ta Ingata rayuwata raheela ta share mata hawaye tace kidaina wannan kukan da kuma tunawa da abunda yawuce washe gari raheela tasa driver yad'auko umma hajara da aunty asabe ya kaisu _matawalle family House_ ta tara iyayyeta maza da mata ta rok'awa umma hajara gafara kowane su ya girgiza da gani yadda umma hajara tadawo gurguwa daga bisani suka ce sun yafe mata kuma sun yabawa raheela had'e da sa mata albarka, na cika alqawali 'yar uwa ta da tayi...... Jeeddah Aliyu🌹 [17/08 11:31 am] Jeeddah Aliyu🌹: 🍆🍆🍆🍆MIJIN 'YAR UWA TAA 🍆🍆 💕love story 2016💕 { part 2} Na Hauwa Shehu Aliyu🌹 1⃣1⃣7⃣ Raheela na zaune a _parlourn kaka_ tana murzawa kaka magani a k'afa Amar ya shigo d'auke da Ainaan yayin da Aryan da Arman suna biye da shi Ainaan takama zillo wai ya ajiyeta yana sauketa, ta falla da gudu ta haye cinyoyi kaka, tace kaka aya mai sikari kaka ta shafi kanta had'e da cewa na'eema kin biyo halin raheela da son zak'i mtss Amar ya ja tsoki cike da jin haushi yace ba dole ba ae duk d'an da kika rena kaka dole yasha zak'i ni kam ba zan yarda ba ki lalata mini yarinya kamar yadda kika lalata raheela yak'arasa magana had'e da shure k'afar raheela. Kaka ta galla masa harara tace to shak'iyi ka zo kayi mini shak'iyanci da kasaba, raheela ta kyalkyale da dariya tace wai sai yaushe Hero da kaka za su daina fad'a"? Amar ya yi murmushi ya d'an shafi sumar kanshi yace ba rana saboda ba za ta daina yi mini shishigi, a cikin al'amura na. Kaka tabe baki tace tashi maza raheela d'auki mayafiki ki ja wannan fitanane miji naki Ku barmin gida raheela ta yi murmushi had'e da mik'ewa tace kaka yau har da Koran mu akeyi"? Ba ke na kora ba wannan miji naki na kora, Amar ya tabe baki yajuya wurin _twins_ yace _come on boy's let's go Home"_ wannan _old woman tagaji da mu_ Arman ya mik'e da gudu ya boye bayan kujera, Aryan kamar zai yi kuka yace _please Daddy ka barmu anan mu kwana wurin kaka saboda gobe ba school tatsuniya takeyi mana mai dad'i gaske irin wance take yiwa mommy a lokacin da take little like baby Ainaan_ Harara raheela ta watsa masa had'e da cewa kai banaso iskanci, Amar ya kyalkyale da dariya kaka na tayashi cikin shagwa6a raheela, tace _please kaka kidaina basu irin wannan labari ae sai su raina ni_ Kaka tace to naji sai da safe raheela ta rik'o hannu Amar tace ka ga Hero zo mu tafi wannan tsohuwar tadaina yayinmu, suka fice daga _parlour_ yaran su suka bisu da cewa _Good night Dad Good night mom_ Amar ne ya amsa musu cikin d'aga murya _Good night kid's_ Suna isa gida Amar yad'auki raheela chak sai faman kyalkyala dariya Sukeyi yadire ta bisa _3 star_ ya chafki bakinta yadinga tsotsa daga bisani yasaketa raheela na dariya tace kai Hero kai fa baka tsofa a wannan shekaru yakamata karage wannan abin Amar yajuyo ta ya matsita a k'irjinshi yace soyayya bata tsofa raheela kamar yadda sonki baya tsofa a cikin zuciyata ina godiya ga Allah {s,w,t} da ya mallaka min ke a matsayin matata ina sonki raheela kece farin cikina kwaciyar hankalina ina alfahari da ke matata. Raheela tak'ara rungume shi tace, bana bakin ciki k'arya alqawali yaya na'eema na son mijinta da nayi domin na cika mata guda d'aya na kula da umma hajara ada wauta had'e da kurciya suka yasa nace banaso ```mijin 'yar uwa taa ``` amma a yanzu na fahince cewa in har babu shi rayuwata ba za ta ta6a inganta ba nima ina sonka Hero kuma zan cigaba da sonka har izuwa k'arshen numfashi na. _Ni kuma 'yar gidan Shehu Aliyu nace Allah sarki soyayya ba abunda yakai ki dad'i da gard'i_ A tsorace suka saki junan su suka kuma mik'e tsaye cikin rawar murya raheela tace Aunty Jeeddah yaushe kika shigo gidanan ne"? shine ko sallama babu kika fad'o mana _parlour_ Allah yaso ki da kinga abunda yafi k'arfinki tak'arasa magana tana murgud'a baki. Na yi murmushi nace maida wuk'a matar likita saboda tun lokacin da aka fara wannan chakwakiyar nake tare da ku kuma yanzu nan zan yi muku sallama na k'ara gaba raheela tayi murmushi tace to sai da safe"? Har na juya Dr Amar matawalle ya kwada min kira ta hanyar cewa aunty jeeddah nayi tsaye chak, yak'araso wurina hannushi rik'e da _check book_ ya yi rubutu akai ya mik'a mini yace ga wannan ki siyawa Baby Minal _chocolate_ hannuna na rawa na k'arbe _check_ d'in zaro idanu nayi, yawun bakina suka kafe sakamako gani abunda ke rubuce a cikin _check d'in_ _2 million naira_ nasaki ihu dad'i na dinga zubawa Hero godiya had'e da addu'ar fatan alkahairi daga bisani na juya na fice daga _parlour_ na sauke ajiyar zuciya nace. ```ALHAMDULILLAH``` _Anan na kawo k'arshen wannan littafi nawa mai suna_ ```mijin 'yar uwa taa part 2``` _ina rok'on Allah {s,w,t} kuskure da ke cikinsa Allah yagafarta min abunda yake da amfani a cikinsa Allah yasa ya amfani al'umma musulmi_ _sarhi akan littafin:- wannan littafi nayi shi ne ba don cin zarafi wani ko wata wannan labari k'iki'ra ne in ya yi kama da labari ki/ka ayi hank'uri akasi aka samu_ Manufar littafin:- ```mijin 'yar uwa taa ``` _Wannan littafi yana fad'akarwa akan masu mumuna d'abi'a bin bokaye da mallaman tsinbo, kuma a wannan zamani wannan mumuna d'abi'ar ta zama ruwan dare, yake 'yar uwa kiji tsoron Allah in kinsan kina aikata wannan d'abi'a Ki tubawa Allah kidaina domin kinga yadda rayuwar umma hajara ta koma tayi k'arko kifi daga ruwa zuwa wuta sai kuma wannan littafi yana fad'akarwa dangane da rashin hankuri da takwali kunga abunda yajanyowa na'eema da a lokacin da ta fahimce cewa, Amar ba ita yakeso ba raheela ce za6i zuciyarshi, tayi hankuri da takwali sai Allah kawo mata Wanda yafi Amar amma sai tasaka son zuciya kunga k'arshen inda son zuciya yakaita gashi ta aure Amar amma takasa mallakar zuciyarshi har ta koma ga ubangiji batada matsayi a zuciyar Amar. Wannan littafi yana fad'akarwa dangane da goyon kaka kasancewa raheela goyon kaka ce ta tashi, batada ingantaciyar tarbiya saboda a wasu lokuta ita take fara tsokanar umma hajara wannan yana d'aya daga cikin dalilin da yak'ara rura wutar kiyayyarta a zuciyar umma hajara Allah yasa mu amfana da fad'akarwa da ke cikin wannan d'an littafi_ ```GODIYA``` _ga wad'anan groups na writer's masu albarka_ _Nagarta writer's association_{Allah ubangiji yak'ara d'aukaka wannan kungiya mai albarka} _Excellent writer's_ _wisdom_ _Extreme_ _online hausa writer's_ _world writer's association_ Ina godiya Allah yabar zumunci ```Ina Godiya ga member's na wadannan groups ``` _ledies novel's world_ _jeeddah Aliyu fans_ _Mrs umar novel's_ _dandali Autar Hajiya_ _zango labarai_ _Matan kwarai_ Jeddah Aliyu na godiya da k'aunar da kuka nunawa wannan littafi. ``` SADAUKARWA``` na sadaukarwa da wannan littafi a gareki besty naa _Fulani Cerdiya_ ```KUN FI KOWA SON WANNAN LITTAFI ``` _Haneefa Usman_ _Autar Hajiya_ _Husna Amir_ _Ammin Jawad_ _kdeey_ _sadiya bala lawal_ Don haka ina gaiyatarku Ku rakani shopping mall mu siyowa baby minal chocolate da _2,Millon's_ da Hero yabani ```GODIYA TA MUSANMMAN``` Ina mik'a godiya ta musanman a gareki _Firdausi Sodangi_ domin kwarin guiwa da kuma yabawa da kike yi a gareni na gode Allah yabar kauna. ```KE D'AYA CE ``` Aminiya ta hak'ik'a _Fatima umar_{Mrs umar} ``` KUNA RAINA ``` Baby amrah Princess amrah Munay Khadija candy Nafisa Anker Shafa'at umar Rabee'at SK Rash Kardam Humairah S A Azeed Stylish Qurattul ayn Zarah bb Ash'nur Atee Ayshat Mazoji Aunty Zarah s gohe Aunty hafsat umar Zainab Hamza Rukayya Dakaratu Zuwaira Dakaratu Billy special Maman afnan Mamanhaneep Maman adnan Maman haneef _ina godiya gare Ku my fans I love you oll_ Sai mu had'u a cikin sabon littafi na mai suna ```Ni da yaya habeeb ``` _urs Jeeddah Aliyu_🌹 adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *