adsense here

👏🏻BISMILLAHIR RAHMANUR RAHEEM...
Ina mik'a godiyata ga dukkan masoyana harma da mak'iyana. Wasunku sunyita tambayana menene na'anar SAD-NAS😄toh ma'anarsa shine sunana da sunan mijina na had'a. Nidai kamar yadda kuka sani sunana SADIYA mijina kuma ANAS, shine na cire SAD - daga sunana, sannan na cire NAS daga sunan mijina shine ya zama SAD💘NAS😜. Masu cewa sunan ya musu dad'i nagode, sannan kuyi hakuri akan rashin sa muku phone number na, kuna raina a kullum kuma ina ganin sak'onninku nagode da soyayyarku agareni😘😘😘
🌺💐TANA🌹RAINA💕💞
By Mmn Shureim
(Sad-Nas)
1-2 Tafiya takeyi tana wasa da sanda a hannunta tana yar wak'anta, maza uku ta gani a gabanta manya suna kallonta tun daga sama har k'asa suna lashe baki😋 d'aya daga cikinsu ya daga nik'af d'in dake fiskarta🙄 suman tsaye sukayi da ganin kyauwun da Allah yayiwa yarinya, nan ya sauke nik'af d'in ya fara shafar gefen hannunta, da sauri ta ture hannunsa ta juya tare da d'iban gudu🏃🏼dariya sukayi sosai sannan suka fara binta da gudu, ba jimawa suka cafkota ta fara kuka tana mena muku dan Allah ku rabu dani, ganin zata tara musu jama'a se d'ayan ya d'aure mata baki ya d'agata se cikin jeji ya ajiyeta kan ciyawi ya fara cire kayan jikinsa, kai take girgizawa tana kuka tana basu hakuri da hannayenta dan babu halin yin magana, amma ina tsindil ya tube😳take ta kawar da kanta gefe tasa hannayenta a k'irjinta, fincike hannun yayi ya warware mata zani yana lashe baki ganin farin fatanta wanda ko tabo babu yana ta sheki, hannu yasa ya cire mata pant ya runk'uro kanta kenan se taji fad'uwan mutum kamar daga sama a kanta yayinda gashin kanta ya rufewa yarinyar ido bata ganin komai se gashin, da alama macece ta fad'o kanta yayinda bayan mace yake jikin ita yarinyar, shikuwa wannan mutum ya fara yiwa macen fyad'e yayinda yake ganin fiskan wannan kakkyawar yarinyan, itadai yarinyar taji mutumin yana ta nishin dad'i amma kuma bai taba jikintaba ko kad'an, bayan ya gamsune se sauran biyun ma sukazo kowa seda ya mata fyad'e dukkansu uku ita kuwa macen se kukan wahala takeyi, dukkansu suna jiyo kukanta harda ita yarinyar, su dai mutanen fiskan yarinyar kawai suke gani tana kuka basa ganin wannan macen, yarinyar ce kawai take ganin macen. Bayan sun gama mata fyd'en se macen ta tashi akan yarinyar tace kisa pant d'inki sannan ki d'aura zaninki kiyita kukan sannan koda kin mik'e kiyita d'ingishi kamar ke akayiwa fyad'e karki damu basa ganina kuma basajin abinda nake fad'a miki ke kadai kike jina da ganina kiyi hakuri da jinin dana samiki a jikinki nayi hakanne dansu tabbatar da sun miki fyad'en nina tafi😊. Take ta bace kamar aljana😳 mutanen sukace ke kyakkyawar yarinya gaskya kina da dad'i sosai musan bazaki iya ko tashiba dan haka zamu kaiki har gidanku amma akan wani sharad'i, idan kika gayawa 'yan gidan to zamu kasheki harma da iyayenki suka fito da🔫dukkansu ukun, 😰se a lokacin ta dawo haiyacinta kuma ta tuna da abinda macen nan ta gaya mata.
[10/22, 7:25 PM] +234 803 863 6764: 🌺💐TANA🌹RAINA💕💞
By Mmn Shureim
(Sad-Nas)
3-4 Take ta kimtsa jikinta sannan ta mik'e tare da taimakon d'aya daga cikinsu, d'ingishi takeyi tare dayin kuka kamar da gaske, ruwa zansa tace dasu d'ayan ya ciro goran FARO ya mik'a mata ta karb'a ta shanye tas, yace a kara mikine a'a tace har suka fito kan titi.
Wata mota suka hango a tsaye a gefen titi, saurayine a tsaye ya juya bayansa yana ta kallon hagu da dama, d'aya daga cikin 'yan iskan yace shikenan ku biyoni a baya, gun wannan saurayin suka karasa yasa masa bimdiga a k'eyarsa tare da juyo dashi suna fiskantar juna🙄, saurayin yace lfy bayin Allah mena muku da zaku samin bindiga akai? D'ayan yace me kakeyi anan, saurayin yace motatace ta tsaya sakamakon zafin da tayi ruwa nake nema kozan samu, d'ayan ya saki hannun kakkawar yarinyan take ta sake jiki ta zube a kasa, se alokacin saurayin ya lura da yarinyan, jikinta duk jini gashi a galabaice take tana d'an zubar da kwalla duk seyaji tausayinta ya kamashi barema yanayin daya ganta kuma tare da wad'anan mutanen da babu alamar tausayi a tattare dasu, yace wannan fa meya sameta haka, d'ayan ya bud'e motar danya hango wata kyakkyawar mata da kuma wata 'yan mata a cikin motan suna zaune, bindiga ya daura musu akai yace dukku fito waje, ba musu suka fito jikinsu se rawa yakeyi, saurayin ya juyo yace me kuke sone, kome kuke so zan baku amma "please karku cutar min da mahaifiyata nd my sister" sannan ita kuma 👉🏻wancan meya sameta haka naga jikinta duk jini? 😆😆😆dariya sukayi dukkansu sukace baka gama tsiratar da family'n kaba har kana iya tuna wata, tunda kana son sani shikenan idan har kana son rayuwar mafily'nka to lallai sekayiwa wa wancan yarinyar fyad'e ko kuma muyiwa mahaifiyarka fyad'e a idanunka harma da k'anwar naka.
😳ido ya zaro yace haba bayin Allah meyasa zakuyi haka, anya kuwa ku musulmaine wani irin magana haka kukeyi, gaskya bazan aikata hakanba, ina rok'onku da kuyi hakuri bazan iyaba. D'ayan ya janye zanin dake jikin mahaifiyarsa tare da janyota kusa dashi, innalillahi wa inna ilaihirraji'un ta fara furtawa tare da cewa haba dan Allah kuyi hakuri nasan dai a haife na haifeku meyasa zakuyi haka, shin zakuso wani yayiwa mahaifiyarku haka, saurayin ya matso da sauri ya d'auki zanin mahaifiyarsa daya fad'i a k'asa Allah yasoma akwai dogon under wear a jikinta har k'asa, ya d'aura mata ya durk'usa har k'asa yana rokonsu, pls ku nemi wani abun daban amma banda wanna, d'ayan yace to shikenan, kokayiwa wancan fyade, ko kuma in fasa kan mahaifiyarka da bindigannan kuma karka dauka ko wasa nakeyi am serious se suka harba bindigansu sama dukkansu tauuuuu kakejin karan, dukkansu sun razana sosai dajin sautin bindingan tunba kyakkyawar yarinyannanba take jikinta ya fara rawa, ita kuwa k'anwan saurayin da gudu ta k'araso gunsa ta rik'o hannayensa tana kuka tana cewa YAH SUHAIL dan Allah karka bari su cutar damu kayi abinda sukeso pls, nan SUHAIL ya juya ya kalli mahaifiyarsa da take kwance a k'asa an d'aura mata bindiga akai sannan ya juya ya kalli yarinyar wanda idanunta kawai yake iya gani sakamakon nik'af dinda yake fiskarta, muryarta ya jiyo tana cewa karka bari a cutar da mahaifiyarka saboda ni dan bakada qacce ta fita na yadda kamin fyad'en😢 a tunaninta k'ila wannan MACEN zata sake zuwa don taimaka mata.
Suhail yace kiyi hakuri mum duk tarbiyan da kuka bani yau gashi zan rushar dashi domin cetonki😰 ina fata zaki yafemin, mahaifiyarsa tace Suhail karka aikata hakan pls yadda bazakaso ayiwa k'anwarka hakaba itama wancan yarinyar ka kalleta amatsayin hafsat k'anwarka nina gama zamanina dama danna mutu ba wani abu bane ka cecesu pls my son, No mum bazan iya rasakiba dan haka zan mata abunda sukeso😰 ahankali ya fara tafiya har inda yarinyar take kwance, se a lokacin suka cire bindigan akan Mum d'insa da kuma hafsat k'anwarsa, yace musu agaskya da kunya inyi mata hakan akan idon mahaifiyata da kuma k'anwata, d'ayan ya juya bayansa cikin ciyawi se yaga wani bukka yace gacan bukka muje ina biye daku, ba musu yarinyan ta mik'e da kyar tana d'ingisawa suna binsu da kallo mahaifiyar Suhail se kuka takeyi tana cewa Suhail dan Allah karka aikata abinda sukeso pls, yana tfy yana bata amsa kiyi hakuri mum na rasa dad bazanso ace na rasakiba kema ki gafarceni mahaifiyata👏🏻. Turata yayi ta fad'a cikin bukkan seya fito yacewa suhail ka shiga kuma inanan a bakin kofa ina ganinku idan kayi wasa da hankalina to wlh sedai ka tafi da gawa biyu da fatan ka fahimceni, shuru suhail yayi tare da juyawa ya kalli su hafsat sannan ya shiga bukka
[10/22, 7:25 PM] +234 803 863 6764: 🌺💐TANA🌹RAINA💕💞
By Mmn Shureim
(Sad-Nas)
5-6 Tana kwance tana kuka tare da k'are mishi kallo tun daga sama har k'asa, tsawa yaji daga bayansa ana cewa me ka tsaya kana kallonta kose mun fasa kan mahaifiyarkane ka dena b'ata mana lokaci kawai ka aiwatar ka fito, ba musu suhail ya fara cire ash suite nashi ya ajiye a gefe, sannan ya cire long sleep fari se ya sake cire dogon wandon suit d'in ya rage daga shi se boxxer da vest, juyowa yayi yana kallon mutumin se yaga yana kallonsa yana murmushi tare da cewa ci gaba mana cire sauran, suhailat yace base na cire sauranba ai sannan ya kai idonsa kan yarinyan gabad'aya tsoro ya cikata, a hankali ya janye zanin jikinta yana kare mata fatarta kallo duk jini, k'yamarta ya kamashi yace a ransa toni suhail yau kuma gani da wata wai zan mata fyad'e kuma 'yar k'auye k'azama taya zan faranema sannan sam bana son jin warin jikinta sam, haka ya yunk'uro kanta nunfashinsu yana had'uwa amma ko kad'an jikinsu bai had'uba, 😳ido ta zaro ganin cewa har yanzu MACENNAN bata zo taimakontaba, shi kuma d'an iskan yana ganin suhail ya rufu a kanta yayi wani irin dariyan mugunta yace ashe dai kaima d'an garine sannan yabar kofan bukkan yad'an tsaya tare da cewa abokansa ai shima d'an garine harya afka mata, hahahahah sukasa dariya yayinda mahifiyarsa ta tsananta kukanta ita da hafsa.
Su kuwa suna daga cikin bukkan suna jiyo abinda ke faruwa a waje, suhail ya juya yaga mutumin baya gun k'ofan bukkan, seya juya yana kallon idon yarinyar yace karki damu bazan miki komaiba amma zan tsaya a hakan danya d'auka ko wani abu na faruwa inaso kiyita kuka da karfinki kinji, 😊nagode lallai kai mutum ne na gari, dad'in muryan nata yaji kuma sam baiji wani wari ko k'arni a tattare da itaba kamar yadda yake tunani, ta katsesa da cewa asheba kyan fiskane dakaiba harda kyan hali😊, kiyi shuru ki dena magana kuka nace kiyi kinji, tace amma har yaushe zaka jure a hakan, yace karki damu ina irin wannan motsa jikin kullum da safe, 😊murmushi ta sakeyi tana jin dad'in kamshin turarensa tana kallonsa har cikin ido shima haka, idanunta sun masa kyau se yaji yanason gannin fiskarta, yace zan iya ganin fiskarki, can setaji kafan mutum yana zuwa, da sauri ta fara kuka mai karfi tana ihu ba tare da hawaye ya fitoba, shikansa suhail seda ya razana bare kuma suna waje, nan suka sake d'iban dariyan mugunta hahahaha lallai guy d'innan shima ya had'u ashe. Kusan 15mint sannan mutum ya dawo yace ya isa haka mana irin wannan kukan da takeyi ko lokacin da muka mata fyad'en dukkammu bati kuka hakaba sannan yabar kofar d'akin.
Suhail ya mik'e da sauri ya rufe mata cinyoyinta da zaninta sannan yasa wandonsa yace zan samu wani d'an abu mai kaifi? Yarinyar ta ciro wani d'an abu mai kaifi da take mak'alawa a jikin gashinta batare data cire nik'af dintaba ta mik'a mishi, karb'a yayi tare da rufe idanunsa ya yanka saman hannunsa da k'arfi, atake jini ya fara fitowa ya dinda bin gun yana d'iga jininsa seda ya zuba sosai sannan ya fara dudduba d'akin kozai samu abunda zai d'aure hannunsa dashi, ita kuwa kuka ta fara dan ta tsorata sosai tace meyasa kayi haka😪? Yace saboda su tabbatar da cewa na miki fyad'e, kuka takeyi tare da zaro d'ankwalinta ta daga kanta batare data cire nik'af d'intaba ta nad'e d'ankwalin ta d'aure mishi hannun tana kuka shi kuwa yanata kallonta tare da cewa karki damu zan samu lfy kuma nagode, tace nine da godiya gaskya kana da kirki bazan tab'a mantawa dakaiba, 😊murmushi yayi mata wanda ya kara mishi kyau yace ga kifiyarki, karb'a tayi ta goge jinin a jikinta sannan ta mayar kanta, yasa kayansa tsaf sannan ya nufi hanyar fita, da sauri tace "Thankyou so much SUHAIL😊" shima murmushi yayi mata sannan ya fita.
Mutumin ya mik'a masa ruwa a galan yace gashi zuba a motarka ku tafi kun tsira. Suhaila ya karba ya nufin gun motan ya zuba ruwan batare daya kalli mum d'insaba, bayan ya gamane yace mu tafi mum kansa a sunkuye dan kunya dayakeji, jiki sanyaye suka shige ciki sannan yaja motan hafsat na zaune a gaba tana kuka sosai su tafi a 260.
[10/22, 7:26 PM] +234 803 863 6764: 🌺💐TANA🌹RAINA💕💞
By Mmn Shureim
(Sad-Nas)
7-8 Ahankali yarinyar ta fito tana d'an kuka tare da d'ingisawa harta k'araso gunsu. D'ayan ya kalleta yace inane hanyar gidanku, tace tacan ne, yace muje mu rakaki dan muga gidan saboda wata ranama mu dawo hahahaha sukasa sa dariya sannan suka kamabinta a baya har suka iso d'an k'auyen nasu daba wani gidaje dewa bare kuma mutane sosai.
Daga nesa suka hango wata yarinya "black beauty" ta fito daga wani gida kuma ta nufosu da gudunta fiskanta d'auke da tambaya ta rungume yarinyar tana cewa "SABREEN" yana ganki haka, meya faru dake k'awata? D'aya daga cikin mutane yace wanine ya mata fyad'e shine muka samota a hanya muka rakota gida inane gidan nasu? 😳Subhanallah Sabreen fyad'e waye shi kuma a ina yake wlh Allah ya isa miki k'awata har abada bazaki tab'a yafe masaba😭 sannan tace mungode da taimakonku gacan gidansu inda na fito yanzu, se sukace to shikenanma base mun k'arasaba tunda munga gidan kuma gakinan seki k'arasa da ita sauri mukeyi suka kalli Sabreen sukace to SABREEN mungode zamu wuce👏🏻 shuru tayi batace dasu komaiba se k'awarta tace godiya me kuke mata kuma ai itace da godiya se anjumanku, yawwa se anjuma sukace da ita sannan suka wuve da sauri.
Har suka dena hangosu sannan sabreen ta juyo ta kalli k'awarta tace ke "MUNIRA" nifa basumin fyad'eba, Munira ta rud'e tace kaman yaya basu miki fyad'eba bayan gashi bakya tfy daidai kuma jikinki duk jini? Sabreen tace mamanki tana gidane, munira tace a'a taje duba mara lfy can mak'ota, sabreen tace muje to in wanke jikina da kuma zanina se in baki lbr, toh muje inji munira mamaki ne a fiskanta sosai suka wuce gidansu munira ta bata zaninta bayan ta wanke jikinta tasa ta wanke zaninma ta shanya tasha ruwa sannan suka zauna ta fara bawa munira lbr tun daga farko har k'arshe. Mamaki da tsorone a fiskan munira tace gaskya SUHAIL d'in mutumin kirkine shida 'yan'uwansa toh ita kuwa wannan MACEN waye ita baki tambayi koda sunantaba? Sabreen ta sauke ajiyan zuciya tace ban iya ce mata komaiba saboda a gigice nake amma dai koma waye ita "TANA RAINA" bazan taba mantawa da itaba munna domin ta sadaukar da kanta domin cetona gaskya dole in sama mata masauk'i, munira tace wani irin masauk'i kuma sabreen, murmushi sabreen tayi tace masauk'i a zuciyata har abada bazan mancetaba domin "TANA RAINA".
Munira tace wannan hakane, sukuma 'yan iskan Allah ya had'asu da wani masifa da fitinar da zatayi sanadin mutuwars... sabreence ta rufewa munira baki da hannunta tace haba munna, aibase kince hakaba kiyi musu fatar shiryuwa mana k'ila su canja halinsu, munna tace ooh don badu miki fyad'enba shiyasa kikace hakako nasan dasu miki dakin tsine musu😄 dariya sukasa tare da tafawa, sabreen tace Allah ya kareki dan seda nazo gidanku akan ki rakani, mama tace ta aikeki shine kawai na tafi ni kad'ai, munna tace kedai dason zuwa rafi yin wanka to ai nikam daga yau na tuba sedai kiyita zuwa ke kad'ai, sabreen tayi dariya tace nima na hakura daga yau😄
Haka sukaita hiransu har zaninta ya bushe ta shirya tsab ta koma gida. Slm mamata slm kakana, wslm suka amsa se kakanta yace sabreen idan kikayi sallama d'ayama ai yayi koko, dariya tayi tare da k'arasawa kusa dashi kan taburma ta zauna tare da d'aukan k'ok'on fura da nono ta bud'e ta fara sha tana cewa nawane ko kaka, mamanta tayi dariya tace seda kika fara sha zaki tambaya, sabreen tace saboda nasan nawane ai mammina. Haka sukaita hira da mamminta da kuma kakanta, bayan isha suka wuce d'aki itada mamminta a gado d'aya suke kwanciya yayinda suke jin d'umin junansu, mammi tana son 'yarta sabreen fiye da komai sam batason wani abu ya sameta saboda rashin mahaifinta, sabreen ta katse mamminta daga tunani da takeyi tace mammina lallai kuna kaunata sosai keda kakana inama ace babana yana raye da gatan nawa yafi haka mammina, wai mammina ciwone ya kashe mahaifina ko menene dan Allah ki gayamin dan yanzu kam aina girma koh? Mammi ta sauke ajiyar zuciya tace sabreen mahaifinki ya rasu ne sakamakon ceto wayanda ba mutaneba😭, sabreen ta tashi zaune tace mammi me kikace😳
[10/22, 7:25 PM] +234 803 863 6764: 🌺💐TANA🌹RAINA💕💞
By Mmn Shureim
(Sad-Nas)
9-10 Mammi tace sabreen kwanta kiyi bacci zuwa gibe semu magan kinji, bamusu ta komata kwanta jiki sanyaye kuma ta kasa bacci hakama mamminta kowacce da tunanin da takeyi a ranta yayin da mammi taketa ta hawaye, itata kuwa sabreen bayan ta gama jimamin mahaifinta seta fara tunanin wannan MACEN da haka har bacci yayi gaba dasu.
Shi kuwa suhail, tunda sunka fara tfy a motan babu wanda yace komai acikinsu in banda hafsat da taketa faman kuka har suka isa gida, bayan mai gadi ya bud'e musu gate ne tare da gaishesu cikin girmamawa,sannan ya tsaya mum da hafsa suka fita seya wuce gun parking ya ajiyemotar sannan ya fito tare da shigewa d'akinsa. Kayan jikinsa ya cire se idonsa yakai gun d'ankwalin Sabreen, shafar d'ankwalin yayi sannan ya kunce a hankali🙄 me zai gani gabad'aya ciwon ya shanye babu jini ko kad'an, gadai alaman yanka harya fara bushewa gun, hankalin suhail ya tashi domin tunaninsa shine idan ya dawo zaije a d'inke masa gun, amma seyaga babu amfanin hakan a yanzu, ya wuce toilet yayi wanka tare dayin Alwala ya fito yayi sallah sannan ya kwanta a gadonsa mai laushi😊 yana murmushi tare dayin juyi akan gadon idanun SABREEN kawai yake gani cikin nik'af dukda tana kuka amma hasken idanunta basu b'uyaba mishiba. Wani gefe kuma mamakine cike a ransa shin ya akayi yanka yayi saurin warkewa haka, meyasa ban bud'e fiskan yarinyannanba, mesa ban tambayi sunantaba, d'ankwalin ya d'auka tare da wucewa toilet ya wankeshi tas da morning fresh ya shanya a toilet d'in sannan ya fito ya kwanta tare da rufe idanu kamar maiyin bacci, magana ya farayi cikin zuciyarsa koma wacece ita zanso in sake had'uwa da ita domin in mata tambayoyi, da haka bacci ya d'aukeshi harse bayan la'asar ya tashi yawu toilet bazo yayi sallan la'asar ya d'auko d'ankwalin ya gogeshi da iron sannan yasa cikin wsll drop nasa seya sa 3kwata da 'yar shet ya nufi daining.
Tunda ya zauna mahaifiyarsa take ta binsa da kallo, shikansa ya lura da hakan bayan hafsat tayi serving nasu seya fara cin abincin batare daya kallesuba har ya gama sannan ya koma palo yana kallon mbc2, bayan su mum sun gamane mai girkinsu taje ta gyara gun tas, su mum suna zaune a palo suhail ya kashe TV sannan ya koma k'asa ya zauna tare da cewa mum nasan abinda yake ranki, amma ki kwantar da hankalinki nisam ban aikatawa yarinyarnan komaiba wlh, ina fata kinsha magungunanki karkisa komai a ranki mum d'ina😊, ba mum kad'aiba harda hafsat seda sukaji sanyi a ransu tare da sauke ajiyar zuciya, mum tace Alhamdulillah Suhail naji dad'in haka Allah ya maka albarka Allah ya kara kareka da aikata abinda ALLAH ya hana ina alfahari da kai sosai d'ana😄 dad'i yaji ya e ameeen mum kema ALLAH ya baki lfy suka sake cewa ameeen hafsat natajin dad'i a ranta kome dalili oho.
Sallama sukaji, suka amsa tare da juyowa, mik'ewa suhail yayi tare da cewa ABOKINA sauk'an yaushe? Yace sauk'an yanzu kanwata jeki zubomin abinci dan yunwa nakeji, da sauri hafsata ta tashi ta wuce kichine, ya k'araso har gun mum ya zauna a k'asa tare da cewa mum ina wuni, mum tayi murmushi tace lfy KAMAL ya hanya ya kuma ka baro mummy, kamal yace lfy lau wlh tace in gaisheku sosai ya jikin naki mum, mum tace toh Alhamdulillah jiki da sauki muna amsawa sannunka da isowa, yawwa mum sannan ya kalli Suhail datun d'azu yana tsaye yana bin kamal da kallo, kamal yace yadai abokina kayi hakuri karkayi fushi ban sanar dakai bane saboda inyi muku zuwan bazata😉, daining ya nufa na zauna tare dacin abinci ko kallon suhail bai k'ara yiba seda ya k'oshi dam sannan yace mum bari naje nad'an watsa ruwa😊, mum tayi dariya tare da cewa toh tana kallon suhail, kamal yace abokina muje ka had'amin ruwan mana kuma albishirinka na samo maka matar aure dan naga ka kusa ka tsufa ba mata😉 aguje suhail ya bishi kamal ya shige d'aki da sauri mum da hafsat se dariya sukeyi😀. Bayan kamal ya fito daga wankane yana goge jikinsa tare da cewa abokina next week zaka tafi fa, suhail yace haba dai gaskya bazanjeba harse mum ta sami lfy sosai, kamal yace tobaganiba ai tunda ina nan shikenan zuwanka yana da muhimmanci gaskya, ajiyar zuciya suhail ya sauke yace toh shikenan ALLAH ya kaimu😒. Kamal yace abokina yana ganka haka, akwai wani abune, suhail yace ba wani abu kawai dai wani abune ya faru yau nan suhail ya kwashe lbr tas ya gayamishi, kamal yace amma basuda imani yanzu dukkansu sukai mata fyad'en? Suhail yace eh sema ka ganta da k'yar take iya tfy wlh abun tausayi. Kamal yace Allah zai sakama kuma naga ka damu sosai, suhail yace eh nadamu abokina dan naso inga fiskanta koda wataran zamu sake had'uwa inaso in taimaka mata dan kamar basu da karfi sosai adai yadda na ganta, kuma d'ankwalinta na guna inaso in mayar mata, kamal yace tobase mu sake komawa ta gunba ko ALLAH zaisa mu ganta, suhail yace jejinefa babu gidaje tagun gaskya sedai k'ila ta ciki, kasan me kamal nidai idanun yarinyar kawai nake iya tunowa, kamal yace toya za'ayi kenan yanzu dama kasan sunantane da abin zaizo mana da sauki amma bakasan komai game da itaba, suhail yace koma menene dai "TANA RAINA" kuma bazan tab'a manta kyawawan idanuntaba sannan kuma.. kamal yace kuma me? Suhail yayi murmushi yace "TANA RAINA" abokina, ok na d'auka zakace kana sontane ai dase ince maka bazai yuba saboda ba cikakkiyar mace bace maza har 3 suka mata fyad'e kaga kuwa babu sauran wani abu a tare da ita. Suhail ya sauke zazzafar ajiyar zuciya tare da rufe idanunsa ya kwanta akan gado yace cewa nayi "TANA RAINA"
[10/22, 7:26 PM] +234 803 863 6764: 🌺💐TANA🌹RAINA💕💞
By Mmn Shureim
(Sad-Nas)
11-12 Washe gari da safe bayan sabreen ta gama sharan gida tas ta gyara ko ina sannan suka zauna a tsakar gida suna suna shan koko da kosai😋, sabreen tace mammina ina sauraronki akan lbrn mahaifina, mammi tace to bari mu gama karyawa koh, to mammi da sauri ta kare ta tattare komai seta dawo ta zauna ta zubawa mamminta ido👀. Mammi tace haba sabreen wannan irin ido da kika samin haka, sabreen tayi murmushi tace nafiso inyita kallon fiskarki yayinda kike magana mammina sam bana gajiya da kallon kyakkyawar fiskarki, mammi tace fiskar nawa har takai naki kyau? To mammi ai kyawunki na d'auko😀, mammi ta mik'e tare da shafar kumatun sabreen tace Allah ya rayamin ke sabreen Allah ya miki albarka bari naje band'aki sena dawo kinji, Ameeen mammina toh ina jiranki, har mammi ta dauki buta zata shige bayi, se sabreen tace mamminah, juyowa mammi tayi ta kalleta seta taso aguje ta rungume mamminta sosai kawai se taji hawaye nabin kumatunta, mammi ta ajiye buta tace sabreen hawayen me haka kuma? Sabreen tace wlh mammina haka kawai naji inaso in rungumeki kuma in zubar da kwalla😥, mammi ta share kwallan idanunta ita tace to shikenan sabreen jeki jirani yanzu zan fito, seda suka rungume junansu kafin ta koma ta zauna. Hayaniya sabreen taji a waje ana cewa maciji maciji, ai da sauri ta fito waje dan ganin macijin, mutane ta gani dewa suna bin macijin a guje ana cewa wannan macijin babbane gaskya zai cutar da mutane idan ba'a kasheba, itama seta fara binsu can setaga macicin ya haura ta katangar band'akinsu tun kafin ya gama haurawa aketa kai mai jifa da duwatsu har an samesa daga wutsiyarsa amma seya haura band'akin, nan jama'a suka ce ya shiga gidansu sabreen muje mu kash...basu karasa maganaba sejin ihu sukayi daga cikin gidan, da gudu sabreen tayi cikin gida dan jin mahaifiyarta na ihu, tana shigowa taga mamminta ta fito da buta a hannu idanunta sun fara juyawa, da sauri mutane suka karaso sabreen ta fara kuka tare da rungume mamminta tana cewa lfy mammina meya samekine, mammi ta fara mata nuni da bayan wuyanta, lekawa tayi taga saran macijine a bayan wuyanta, seta hango macijin yana nema hanyan guduwa, da sauri tace gashican ku kasheshi ya ciji mahaifiyata, ai kuwa macijin kamar yaji abinda akace ya juya zai koma ta katangar, lokacin mammi tana ta cewa sabreen ki kula da kanki ki rek'e ibada da gaskya, mammi kiyi shuru zamu kaiki gun malam dare yanzu babu abinda zai sameki se kuka takeyi tana rungume da mamminta, saukar mutum taji daga sama ammab kuma bataga komaiba, da sauri mammi ta d'ago kanta dan taji wata irin murya yana cewa kiyi hakuri mammi nazo a makare macijin wannan MACEN ta sari kansa batare dakan ya rabu da jikinsaba sannan tazo hargun dasu mammin suke, su kuwa jama sunga dai macijin akan garu bai saukaba kuma basuga wani nauni a jikinsa dan haka sukayita kai masa sanda da duwatsu da kuma sara, take macijin ya fara fidda jini a jikinsa nan sukaita murna sun kashe maciji, basusan MACEN NAN bane ta kashesa. Mammi takai dubanta ga MACEN, macen tayi murmushi tace kiyi hakuri mammi seyau Allah yayi zaki ganni nine dai wannan yarinyar da mijinki ya rasu ta dalilina, nayi miki alk'awarin kula da sabreen insha Allah bazan bari a cutar da itaba😰, murmushi mammitayi😊 tare da cewa nagode, sabreen ta kalli mammi ta kalli inda mammi take kallo ita dai jama'an da suka kashe maciji kawai take gani, sabreen tace mammi ba godiya zaki musuba ku taimaka mu kaita gun malam dare, hawaye itama macen tafarayi dan yadda taga mammi nayi dan mammin ne kad'ai take kallonta. Atake MACEN ta b'ace,sannan mammi ta juyo tana kallon sabreen tace base ankaini ko inaba sabreen kicewa kakanki ya baki labarin mahaifinki sannan kuma sabreen ki kulada kanki ina kaunarki sabre....😭😭😭
Allahu Akbar! Kulli nafsi za'ikatil maut. Shikenan mammi ta tafi, kuka soai sabreen takeyi tare da jama'an gurin, dakyar aka d'aga sabreen daga jikin mamminta aka kaita gidan su munna😰😰😰
[10/22, 7:25 PM] +234 803 863 6764: 🌺💐TANA🌹RAINA💕💞
By Mmn Shureim
(Sad-Nas)
13-14 Suhail da kamal ne a hanyan tfyansu kauyen su Sabreen, suna tafe suna hira har suka iso daidai gurin daya had'u dasu sabreen, se uace kamal a daidai nan ne amma dai mu kara gaba kadan, ahankali,suke tfy se suka hango hanya shiga garin sukai tfy kad'an se suka hangi kakan sabreen yana komawa rike da cefene a hannunsa, gunsa suka tsaya da motan tare da dayi masa sallama, bayan sun fitone suka gaishesa cikin girmamawa sannan sukace baba dan Allah muna tambayane, yace toh ina jinku, suhail yace wata yarinya nake nema ko Allah yasa ka santa, kaka yace menene sunanta? Suhail ya kalli kamal se kamal yace wato dai baba muma basusan komai game da itaba kawai dai mun gantane tanan tana sanye da riga da zani da kuma bak'in himar sannan tasa nik'af a fiskanta, kaka yace to gaskya bayin Allah bazan ganetaba, dama ace kun gayamin sunantane ko sunan mahaifinta ko kuma kamanninta,toda zan iya ganewa, suhail yace baba yarinyar an mata fyad'e jiya jiyan nan kuma dai muna kyautata zaton atanan take, kaka yace fad'e kuma subhanalillah to gaskya bata nan bane, domin duk abinda ya faru a kauyennan baya b'uya a masallaci ake sanar da koma menene, kamal yace to ai k'ila baza a iya sanar da magana irin na fyad'e ba, kaka yace za'a sanar ina tabbatar muku da cewa babu abinda yake b'uya a kauyennan namu, wai samari me kuke nema agun yarinyarnan ne, kamal yayi saurin cewa dama daga cikin gari muke, muna neman masu aiki ne, kaka yace wani irin aiki kuma, kamal yace mata dai wanda suke aikin wanke wanke da shara da kuma girki za'a dinga biyansu a wata. Kaka yace haba da gaske, ina da jikata nasan zatayi farin cikin hakan dan ta dad'e da gama secondary tana so taci gaba da karatu amma bamu da hali, tayita neman aikin a kauyennan amma bata samuba, sedai kuma aiyukan daka lissafo sunyi yawa, Suhail yace a'a dama girkine kawai zata dingayiwa mahaifiyata dan bata da lfy, kaka yaji dad'i sosai yace indai wannan ne shikenan jikata ta iya girki amma na gargajiya ne ko kuma ince namu na karkara sam bata iya naku na birnineba. Kamal yace ba damuwa muma ai muna cin abincin gargajiyan sosai dan haka ba matsala zamusa a koya mata😊. Kaka yace to shikenan kud'an bani lokaci inyaso seku dawo daga baya koh? Suhail yace to shikenan mun gode sosai baba, kaka yace bakomai nine da godiya nasan jikata zatayi farin ciki sosai dan haka sekun sake dawowa...wasu samarine suka karaso a guje suna haki suna cewa kaka gara da muka had'u dakai, Allah yayiwa mammin SABREEN rasuwa yanzu yanzun nan shine aka aikomu donmin muzo mu kiraka, 😳Innalillahi wa inna ilaihir raji'un dukkansu suka amsa, kaka yace me kace SALE, Mammi ta rasu😰? Sale yace eh kaka macijine ya sareta a bayan wuyanta kuma harta cika😭. Kaka yace ina sabreen jikata take a wani hali take ciki? Suhail ya kamo hannun kaka yace baba shiga muje tare, ba musu suka shige gabad'ayansu suka isa har kofar gidan inda suka iske mutane a cike. Fitowa sukayi dukkansu suka wuce cikin gidan, lokacin har matan makota sunyi mata wanka an suturceta kaka ya isa yayita mata addu'a sannan aka fito da gawanta zuwa waje nan akai mata sallah aka d'auketa dan kaita gidanta na gaskya sega sabreen ta fito a guje tanata kuka tana cewa kaka dan Allah karku tafi min da mammina ina sonta wlh karku kaimin mammina rami dan Allah ku tausayamin ita kad'ai ta ragemin fa kaka😭. Kowa ya tausayawa sabreen musamman kaka da iyayen munira, munirane ta biyota da hijabi danko d'ankwali babu akanta bare takalmi, gashin kanta duk ya tattashi kamar wata mahaukaciya, bayan munna tasa mata himar d'inne se take k'okarin janyota amma ta kasa, kaka yace da suhail dan Allah yaro taimaka ka mayar min da ita gida kaji, ba musu suhail ya kamo hannunta yana kokarin maidata gida seta gantsara masa cizo tana cewa dan Allah ka sakeni zasu tafimin da mammina nefa nika sakeni😭. Kuka sosai takeyi hakama munira, Suhail ya rasa meke masa dad'i sam bayaso yaji mace na kuka, ahaka har suka k'arasa kofar gidansu munira wata mata ta riko hannunta suka k'arasa da ita cikin gidansu muniran. Shi kuwa suhail hannunsa yayi jahjazir dan cizon da sabreen tayita mishi, binsu yayi mak'abartan akai mata komai sannan suka dawo sukai musu gaisuwa se suka tafi suna masu tausaya musu sosai😔😔😔
[10/22, 7:26 PM] +234 803 863 6764: 🌺💐TANA🌹RAINA💕💞
By Mmn Shureim
(Sad-Nas)
15-16 Bayan su suhail sun dawo gidane suka sami mum a palo, bayan sun zauna ne kamal ya dauki ruwa a frigj yasha sannan yamikawa suhail mayasha, mum tana ta binsu da kallo tace lfy kuwa kodai baku sami mai girkin bane? Kamal yace mum samu mum nan dai suka bata lbrn abinda ya faru, sosai mum itama abin ya bata tausayi, tace Allah sarki Allah ya jikanta yanzu dai za'a d'auki lokaci kafin tazo, can se idonta yakai kan hannun suhail, tace suhail me nake gani a hannunka, suhail ya shafi gurin yace cizon da yarinyan tayitamin ne lokacin dana rik'e hannunta, shi kansa kamal baisan da batun cizonba se yanzu dayaga hannun suhail yayi jah kuma ya kunbura, mikewa suhail yayi ya shiga d'aki ya watsa ruwa sannan ya fito ya goga mantileta a hannun nasa seya kwanta yana tunanin abunda ya faru, kamal ne ya shigo shima wankan yayi,yazo ya zauna kusa da suhail fiskar sabreen kawai yake gani dana munira, mamakin irin kyawu na sabreen yakeyi, yace suhail amma kaga fiskan sabreen kuwa, gashi dai kauyene amma har ana samun kyawawa haka, gaskya irin kyawun sabrin sedai a kasar larabawa da indians bade nigeria ba.
Suhail yayi murmushi yace abokina ni gaskya banganta sosai ba, saboda gabad'a kukanta ya d'aga min hankali, kamal yace dama na tuna hakan a raina wlh, yauzu me abin yi? Suhail yace se ranan da za'ayi uku semu koma muyi musu gaisuwa, tunda wani sati zanyi tfy zuwa ranar da za'ayi bakwai seka sake komawa kaji me kakan nata zaice. Haka za'ayi suhail Allah ya kaimu.
Haka sabreen ta kasance cikin kuka koda yaushe, nasiha sosai malaman kauyen nasu suke mata harta dena kukan, amma dai ba'a rasa ganin hawaye a fiskanta. Kullum zaka ganta tare da munira dan a gidansu take zaune, maganganu masu kwantar da hankali munna take mata harta d'an ci abinci kad'an, amma idanunta sun kubura dan kukan mamminta.
Yau ne za'ayi uku, suhail da kamal suka shirya cikin fararen shadda dasu akayi addu'oi sakamakon sunzo da wuri, bayan an gamane suka sake keb'ewa da kakan sabreen sukace sunaso su mata gaisuwa, kaka da kansa yaje ya kirata, himar suka saka ita da munira suka fito lokacin kaka yaje gaisawa da wasu. Kamal ne ya fara magana yace sabreen ya hakuri, kanta ta d'ago tace Alhamdulillah tana kallon kamal din, yace Allah ya jikanta, tace ameen sannan ya juya gun munira suna gaisawa se suhail yace sabreen ya hakuri, kai ta d'ago don kamar taso ta gane muryarsa, idonsu na had'uwa ta ganeshi tana masa kallon mamaki, Alhamdulillah tace dashi, yace toh Allah ya jikanta da rahama, ameen tace nagode sosai harda yar mirmushinta😊. Suhail ma kallonta yakeyi har cikin ido, se kuma ya kau da kansa yace kamal muje koh, kamal yace to sabreen ya sunan kawarki ne, sabreen tace sunanta munira, ok dukkanku kuna da suna masu dad'i mu😊, sabreen tace mungode Allah ya bada lada tana kallon suhail shida yake kokarin wucewa gun motansa yace ameen mum d'inmu tace amik'a mata gaisuwa agareku, sabreen tace mungode sosai, murmushi suhail yayi mata sannan ya kira wasu yara tare da bud'e but na motarshi yara suka fara shigowa da kayan abinci juice, taliya, indomie dasu buhun shinkafa. Sabreen ta kalli kamal tace wannan fa, kamal yace sadakace muka kawo muku, hawayene yake fitowa daga fiskarta daidai lokacin suhail ya karaso, hanki ya ciro a aljihunsa ya mika mata, hannu tasa ta karb'a tana kallonsa har cikin ido tana zancen zuci, duk lokacin da nake cikin wani hali se in ganka agun ya akayi kazo nan kuma? Suhail ne ya katseta da cewa shide mamaci babu abinda yafi bukata irin addu'a kukanki azabane agunta sabreen, dad'in zancen nashi taji atake tare hawayenta da hankinsa sannan ta mika mishi tace mungode sosai Allah ya bada lada, ameen sukace se suhail yace ki rik'e nabar miki😊, itama murmushin tayi tace se anjumanku sannan tajawo hannun munira suka wuce gida. Kamal se binsu da leke yakeyi, suhail ne ya janyo rigansa yace inaga dai ba k'alau kakeba, gaisuwafa mukazoyi ba kallonsuba malam, dai dai lokacin kaka ya k'araso yana musu godiya sannan sukaci gaba dayin magana. Sabreen kuwa mamaki takeyi ya akai suhail yazo nan🤔, maman munirace tace sabreen wannan fa suwaye suka kawo, sabreen tace sune wanda muka gaisa dasu yanzu nima ban sansuba sedai mu tambayi kaka idan ya shigo k'ila shiya sansu😉.
Bayan kaka yayi sallama da kowane saiya shigo gidan su muniran, nan gaya kayan abinci kam dewa. Baban munirane yake tambayan kaka suwaye suka kawo wannan sadakan haka? Nan kaka ya kwashe lbrn had'uwansu dasu suhail tas ya gaya musu. Munira tayi saurin juyowa ta kalli sabreen, sabreen ta kyafta mata ido😉 sannan ta fara murmushi a zuciyarta tace to meyasa yake nemana, kodai d'ankwalina zai bani? Alhamdulillah tunda baiga fiskanaba, kuma koda naje yin aiki a gidansu bazan tab'a sanar dashiba tunda nidai nasan ba'amin fyad'eba kuma ina farin ciki zan koma makaranta dan haka na amince zanyi musu aikin☺
[10/22, 7:26 PM] +234 803 863 6764: 🌺💐TANA🌹RAINA💕💞
By Mmn Shureim
(Sad-Nas)
17-18 Sabreen da munirane suna zaune a d'akinsu bayan sunyi sallan isha suna cin abinci, munira ta kalli sabreen tace dama shine suhail d'in? Sabreen tace eh shine bai ganenibane saboda nik'af ne a fiskata ranan. Munira tace to ai yakamata ki sanar dashi tunda kinga nemanki ne yasa suka sake dawowa nan d'in, sabreen tace a'a munna wannan maganar sirri ce tsakanin nida ke pls, munna tace to ai shikenan kika san koya kyasa ne yasa ya biyoki, gashi da alama masu haline kinga shikenan mun fito fari😜, dariya sukayi dukkansu sannan sukaci gaba da hiransu.
B'angaren suhail kuwa, tunda suka dawo kowa da tunanin da yakeyi, hafsat ne tazo ta samesu a palo tace yah suhail ina kukajene inata nemanku, suhail yayi murmushi yace munje gaisuwa ne hafsat akwai wani abu ne, a'a kawai dai dan ban ganku bane. Kamal yace nidai zan tafi gida seda safenku, suhail ya tashi ya rakasa hargun mota sukai sallama sannan ya dawo gun mum sukaita hira har zuwa 9pm kafin suka wuce donyi bacci. Shidai suhail yana ta kallon idanun sabreen a ransa dan yayi mishi kama dana wannan yarinyar, sedai na sabreen sun kumbura kuma sunyi jah, to shine dai yake kokonto akan kila kamace kawai, kuma kaka ya tabbatar musu da cewa babu yarinyar da akayiwa fyad'e a kauyen, ya shiga rud'ani sosai da haka yayi bacci...
Yau wata guda kenan da rasuwan mammin sabreen. Shikuwa Suhail yana can pakistan kusan 3week kenan. Kamal ne a kofar gidansu munira yana jiran fitowar kaka da sabreen, can segasu sun fito suna rungume da juna suna kukan rabuwa, maman munirane taketa basu hakuri tana cewa munna kiyi hakuri aiba rabuwa kukayiba 'yan watannine kawai zatayi seta dawo kinji, da kyar dai suka rabu kamal ya bud'ewa kaka gaba sannan sabreen ta shiga baya suka tafi tanata yiwa munira bye tana kwalla. Tunda suka fara tfy sabreen taketa kuka har suka iso wani gida mai kyau, hon kamal yayi aka bud'e suka shiga, bayan motan ya tsayane kamal yaje ya bud'ewa kaka dan sabreen kam harta fito tana rik'e da yar jakanta, kamal yace bissimillah kaka muje, kofa ya bude sika shiga k'aton palo mai kyan gani, anan suka zauna kamal yace sannunku da zuwa kaka😊, kaka yace yawwa sannu kamal, ruwa mai sanyi ya kawo musu tare da juice ya zuba musu, ahankali suka karb'a suka sha tare dayi mishi godiya. Kamal yace kaka nan gidan mahaifinane amma Allah yayi musu rasuwa shida mahaifin suhail a k'asar saudiya, iyayenmu aminan junane sosai suna business a wani kamfani dake pakistan, lokaci lokaci suna zuwa duba kasuwancin nasu. bayan rasuwansune mahaifiyata tayi aure a pakistan d'in, inda ni kuma nake zaune a gidan mahaifina, nida suhail mukaci gaba dayin business kamar dai yadda iyayenmu sukeyi, idan naje wannan karon, wani karon kuma suhail ne yake zuwa, mahaifiyar suhail tak'i yin aure sam tana zaune damu anan da kuma 'yar yayan baban suhail wato hafsat, itama marainiyace dan bata da uwa bare uba. Mahaifiyar suhail ta rik'e hafsat kamar 'yarta na cikinta, inda mu kuma muka zame mata yayyu. Matar da take musu girki d'anta ya samu aikin yine shine yace mamansa zata dena girki, shiyasa muke neman wanda zata dinga musu girki ana biyanta duk wata. Kaka yayi ajiyar zuciya yace Allah ya jikansu da rahama suka amsa da ameen dukkansu. Kamal yace na kawoku nanne saboda kace sabreen bata iya girkin zamaniba sena gargajiya, shine nakeso ku zauna anan koda na tsawon wata biyu ne na samo wanda zata dinga koyawa sabreen girke girken zamani idan ta iya sena kaiku gidansu suhail koya kagani kaka? Kaka yace bakomai kamal na fahimceka kuma na amince danna yaba da halaiyarku nasan bazaka cutar damuba zamu zaunan anan d'in harse ta gama koyon. Kamal yayi murmushi yace to alhamdulillah kaka ina tabbatar maka da cewa bazan tab'a cutar dakuba shiyasama nace mu taho tare dakai koda ruwa seka dinga ba flawer kaima ana biyanka. Godiya sosai kaka yayi sannan kamal yace muje in nuna muku masauk'inku, tare suka mik'e sabreen tana binsu a abaya, d'akin mummynsa yaba sabreen, sannan yaba kaka d'akin babansa, manyan d'akunane da komai a ciki, murna sosai sukayi tare da k'arayin godiya.
Kamal ne kwance a d'akinsa ya kira suhail a waya yace abokina se nanda 2month su kaka sasu zo, suhail yace toba damuwa Allah ya nuna mana, kamal yace amin sannan sukaci gaba dansu. Bayan sun gama wayanne kamal yace bazan iya sanar dakai suna gunaba abokina, harse sabreen ta k'ware sosai da girkin zamani anan, insha Allah gobe zanje inyi musu cefene sosai zuwa jibi RUKAYYA zatazo ta fara koya miki sabreen, da wannan shawaran kamal yayi bacci tare da jin dad'i a ransa wanda bansan dalilin saba😊😊😊
[10/22, 7:26 PM] +234 803 863 6764: 🌺💐TANA🌹RAINA💕💞
By Mmn Shureim
(Sad-Nas)
21-22 Bayan sabreen ta gama karyawane taje tayi wanka tasa d'inkin doguwar riga na atamfa ta d'aura d'ankwalinta sannan tasa farin himar komai bata shafaba ta fito. Kamal ya shirya cikin blue shet da black jeans yana zaune a palo yana jiran fitowanta, can segata ta fito da murmushi a fiskanta tace hamma kamal na shirya, kalonta yayi tare dayin murmushi yace toh muje, atare suka fito lokacin kaka yanaba flower ruwa sunata hira da mai gadi,segasu sabreen sun fito tace kaka zamuje mu dawo, kaka yace toh sabreen sekun dawo. Tunda suka fara tfy babu wanda yace komai acikinsu har suka karasa super market, nanne kamal yace muje sabreen😊, a hankali ta fito suka shiga se kallo takeyi dan bata tab'a zuwa super market ba. Kayan abinci suka saya sosai, sannan kamal ya kaita gun kayan sawa yace ta d'auki duk abunda taga ya mata kartaji kunya, nan sabreen tayita d'iban atamfofi da material da kuma dogayen riguns, ta kalli kamal taga yana can nesa da ita, gunsa ta nufa tace hamma kamal zan iya d'auka ko wanne 2? Murmushi yayi yace ko 5 5 nema ki dauka kinji😊, murmushin itama tayi sannan tace nagode ta juya yana binta da kallo yana murmushi, komai 2 take d'auka wai ita da muniranta. Bayan sun gama da kayane yace ta biyosa suje gaba, sun isa wani gun maiyukan shafawa suka nufa da turaruka, NATURAL HONEY shine mai d'inda take shafawa ita da munna, dan haka shima ta d'auki 2 sannan ta d'auki turaren FASIO shima 2 dasu body spray, kamal yace kayan kwalliya fa, sabreen tace sedai in d'aukawa munna danni bana kwalliya, murmushi yayi yace koda gazal da janbaki da hoda nedai ki dauka, dariya tayi tace hamma kamal ai to na d'iba kayan kwalliyan gaba d'aya kenan, yace eh idan kina kwalliya zakifi haka kyau, ba musu ta d'iba suka d'ibi takalmi da jaka, sayayya dai sukai sosai sannan suka wuce gun tela aka bashi d'in kaya kala 24 nata dana munna. Daga nan suka wuce gida, kaka ya tayasu shiga da kayan komai aka shiryashi a store, kayan,tea kuma suna daining drinks a frij, komaidai gun zaman suna nama akai kaisa babban friza. Sabreen ta nunawa kaka irin sayayyan daya mata ita da munna tace kuma munbada d'inkin kaya, kaka yayita masa godiya dasa masa albarka hakan yayiwa kamal dad'i sannan yabaiwa kaka takalma da turare yace kayanka anjuma zankai makasu d'inki, godiya sosai sukayi sannan kamal yace shizai fita zaije ya duba mum d'in suhail da hafsat ze zuwa dare zai dawo sabreen ki dafawa muku koma menene kinji, toh seka dawo😊.
A gidansu suhail kamal ya yini yayita bacci harseda yayi sallan isha sukaita hira kamar yadda suka saba sannan ya koma gida. Lokacin 8:30pm kaka suna zaune a palo suna kallon sunna TV kamal yayi sallama tare da shigowa, bayan ya zauna ne yace kaka sannunku da gida😊, yawwa kamal sannu da dawowa yaka barosu, lfyansu lau wlh, sabreen tace sannu da zuwa hamma kamal ga abincinka akan daining, yawwa sabreen ta bari naje nad'an watsa ruwa senazo naci girkin k'anwata😀. Bayan yayi wanka ya fitone yasa jallabiya tare da fesa turare ya wuce daining, sabreen ta mik'e taje ta zuba mishi tuwon shinkafa da miyar egushi yaji manja da dry fish ga nama😋, tunda sabreen ta bud'e kulan kamshi ya daki hancinsa take nyawunsa ya tsinke, da bissimillah ya fara cin abincin yana lumshe ido☺😊, sabeen ya kirata, tace na'am tare da mik'ewa, irin wannan miya mai dad'i aibase a samo mai koya miki girkiba domin ni ban tab'a cin miya mai dad'n wannanba, dad'i sosai taji tana dariya tare da cewa nagode amma ina bukata dai akoyamin wad'anda ban iyasuba na zamani. Kamal yace badamuwa gobe zatazo ta fara nuna miki kinji, tace toh Allah ya kaimu goben yace ameen.
Washe gari da safe RUKAYYA tazo bayan sun gaggaisa ne se suka wuce kichine da sabreen suka fara had'a breakfast, duk abinda RUKAYYA takeyi idon sabreen nakai har suka gama sukayi breakfast gabad'ayansu kuma sunji dad'in girkin nata😋. Haka sukayi na rana suka sake yin na dare, kullum kuma RUKAYYA so 3 takeyin abinci wato safe rana da kuma dare, seda tayi girki harna tsawon 1 week sannan tace sabreen ta sake maimaita duk abinda ta dafa na tsawon satin. Tsab kuwa sabreen tayi kamar yadda RUKAYYA takeyi kuma yayi dad'i sosai, Aunty rukayya shine sunan da sabreen take kiranta dashi, cikin k'ank'anin lokaci suka shaku da juna sosai kuma sabreen taci gaba dasa hankali akan koyan girkin. Shikuwa kamal dad'i yakeji sosai yana zuwa dubasu mum kullum dan acanma yafi zama se dare yake dawowa.
[10/22, 7:26 PM] +234 803 863 6764: 🌺💐TANA🌹RAINA💕💞
adsense 2 here