adsense here
Copied By
HAYATU BABA ZUBAIRU
(admin
Novels villa
Duniyan novels
Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
And
Cool novel, makeup and cooking)
WHATSAPP NO:
+2347039625239
YAYA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
ﺍﻟﺒﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮ ﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮ ﺣﻴﻢ .
ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺍﻏﻔﺮ ﻟﻲ ﺫﻧﺒﻲ ﻛﻠﻪ، ﺩﻗﻪ ﻭﺟﻠﻪ، ﻭﺃﻭﻟﻪ ﻭﺁﺧﺮﻩ
ﻭﻋﻼﻧﻴﺘﻪ ﻭﺳﺮﻩ.
ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺻﻞ ﻋﻠﻰ ﻣﺤﻤﺪ ﻭ ﻋﻠﻰ ﺃﺯﻭﺟﻪ ﻭﺫﺭﻳﺘﻪ ﻛﻤﺎ
ﺻﻠﻴﺖ ﻋﻠﻰ ﺁﻝ ﺇﺑﺮﻫﻴﻢ . ﻭﺑﺎﺭﻛﺖ ﻋﻠﻰ ﻣﺤﻤﺪ
ﻭﻋﻠﻰ ﺃﺯﻭﺍﺟﻪ ﻭﺯﺭﻳﺘﻪ ﻛﻤﺎ ﺑﺮﻛﺖ ﻋﻠﻰ ﺁﻝ ﺇﺑﺮﻫﻢ،
ﺇﻧﻚ ﺣﻤﻴﺪ ﻣﺠﻴﺪ .
GATARWA
Dukkan yabo ya tabbata ga Allah. Ina
godiya a gare sh’i, ina neman
taimakonsa, ina neman gafaransa, kuma
ina neman tsarinsa daga sharrace-
sharracen rayukanmu da mitagyn
ayyuka. Wanda Allah ya sh’irye sh’i
babu mai b’atar da sh’i, wanda kuma ya
b’atar ba mai sh’iryar da sh’i.
Ina shaidawa babu abin bautawa da
gsky sai Allah, shi kad’ai, babu abokin
tarayya gare sh’i. Ina shaidawa cewa
Muhammadu bawansa ne kuma
manzonsa ne. Ya Allah kayi tsira ga
wad’anda suka bish’i da ky’aky’awan
kw’aikw’ayo har zuwa ranar kiyama.
Kuma ka musu aminci, aminci mai yawa
Ameen.
SADAUKARWA
Na sa daukar da wannan littafi mai sun
YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU, ga
Mummy’s d’ina Khadija’s.
GODIYA
godiya mai d’imbin yawa gareku, da
bazarku nake taka rawa a duniyar
Rubutu, Allah ya barmu tare.
Maryam .S. Bello
Maryam Alkali Mamu(Mrs Jabo).
Page-1~5.
Tari wanki ne a gabanta, sai faman
wanke su takeyi, kalo d’aya zaka mata ga
gane ta gala baita sosai, har k’arfin har
bata jin karfin jikinta.
Gwaggo ne ta taho da wasu kayan
wankin ta kara mata, tace “Khadi maza-
maza kiyi sauri ki wanke ma Beeba
kaya, zata gidan Innarku.
A wahale na d’ago nace “Inna ga
wasu sabbin kayanta can na wanke su,
sun bushe tasa su, kuma suna da ky’au,
gash’i nayi wankin da yawa na gaji.
Gwaggo wani uwar ashar ta narko,
wanda ni Rash bansan lokacin da nayi
baya da sauri ba.
Shako ta Inna tayi tace”dan jakar
ubanki ni zaki fad’a ma kin wanke
wasu, kuma har kina iya cewa kin gaji.
Eh! Lallekam yau zaki gwadan ke yar
Zamani ce, ban isa dake ba ko?.
Khadi cikin muryan kuka tasoma
cewa”dan Allah! Gwaggo kiyi hak’uri
wlh ba da wara manufa na fad’i hakan
ba.
Gwaggo kara shaketa tayi tace”ko
uwar ki ma bazata mayar min da
martani ba. Kafin Khadi tayi magana ji
kake tass tass tass ta wanke ta da mari
har sau uku, dukanta tafarayi ta kota
ina.
Wayyo ni kaina Rash na tausaya
ma Khadi, don ga alama fuskan gwaggo
nan bata da tausayi ko kad’an
Taku a kullum mai k’aunar ku
ﺭﺍﺷﻴﺪ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-6~10.
Gwaggo sai da tayi likis ma Khadi kafin
ta ky’aleta, tace”wlh sai kin gama
wankin nan yau ko na miki dan banza
duka, sha-sha kawai, mts tayi tsaki ta
nufi cikin d’akinta.
Khadi kam kuka tasha ga wani
yunwan da ke murd’amata ciki. Kama
cikin tayi ta tamke da d’an kwali abunka
da Khadija maganin Maza cikin dakiyar
zuciya ta fara wankin
, da ikon Allah kafin akira Sallah la’asar
ta gama.
Gwaggo ta fito da abinci a d’an
k’aramin kwano wanda ko d’an yaro
bazai ish’esh’i ba. Ta turo mata kwanon
ta juya tayi d’akinta ko tausayin
Yarinyan nan bata ji ba. Ga uban aikin
da ta mata a cikin gidan kamar jaka.
Malam Ahmadu ne ya sh’igo da
Sallamansa, in donsa ne ya sauk’a kan
Khadi dake kwance tamkar wanda aka
d’aura ma dutsin dala da gauron dutsi
aka.
Da sauri ya k’arasa gurinta cike
da tausaya wa, ya tallabo ta yace “Mama
na ya dai? Mai ya same ki na ganki
haka? .
Gwaggo ta fito cike da masifa
tace”komai ne ya same ta ko zaka karb’a
mata ne, sai in sani.
Cike da b’acin rai Malam Ahmad
ya nufo ta, yace”kee Hauwa wlh ki
kiyaye ni zan sas-saba miki akan
Khadija sam ba kya tausayin yarinyan
nan.
Gwaggo tace “ina ko zan tausaya
mata ba sanin zafinta nayi ba bare na
san miye tausayi.
Malam yace”duk aikin da take
yi a gidan baky’a gani ko?. Kuma ba
ky’a sanya yar cikinki.
Wannan yarinya Yata ke a gun mu, duk
irin rikon da muka mata Allah zai
tambaye mu, Hauwa kiji tsoron Allah.
Gwaggo tace”ehehe wa’azi
zakamin ai tsoron Allah kulum cikinta
muke, yar wani ba yata bace nawa
kawai na san, fuuu tayi d’aki in ka gama
sai ka sanar min.
Taku a kulum mai k’aunar ku
ﺭﺍﺷﻴﺪ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-11~15.
Cikin ta kaici yazo ya tallabi Khadi ya
d’agata sai a lokacin ya kalli d’an abinci
da gwaggo ta bata.
Taburma ya d’auko a d’akinsa ya sh’in
fid’a mata, ya zaunar da ita.
Kular abincinsa ya kawo mata
tare da juye ruwa mai zafi ya had’a
mata Lipton ya bata da kyar ta iya sha.
Abicinsa ya kara mata, sai da ya
tabbatar ta kosh’i kafin ya ci sh’ima.
Khadi ta mik’e jiki ba kwari ta
nufi rijiya ta d’ebo ruwa ta nufi bayi,
wanka tayi ta fito, ta sha fa mai kayanta
masu d’an kyau ta saka ta dawo waje
gun Malam don gudun bala’in Gwaggo.
Malam yace”Mama nah bazan
fasa miki nasiha ba, inaso ko kasance
mai yawan hak’uri kinga halin Gwaggon
ku kullum Addu’a nake mata Allah yasa
ta gane gsky.
Khadiya duk halin da kika samu kanki,
ki kasance mai hak’uri zakici riban
rayuwanki. Kai ta d’aga masa alamae
Eh!.
Heeba ce ta sh’igo da Sallaman ta,
cikin fara’a ta k’araso gun su, sannu da
gida ta musu kafin tace”Addah ina ta
sauri inzo in tayaki aiki, da aka tash’i a
makaranta, ban samu abun hawa ba,
Gash’i har kin gama.
Khadi tayi murmushi tace”ba
komai k’anwata, ya makaranta?.
Alhamdulilah! Ki d’auko abinciki kici to
Adda.
Malam yana jin dad’in yanda
yaransa suka had’a kai, baran Beeba da
sam bata gado halin uwarta ba, heeba ya
rinya ce mai hankali kamar Khadi.
Sabanin Rabi da ke ji da taken rash’in
kunya, halinta sak na uwarta hatta kama
da Gwaggo take kama.
Gwaggo tafito tsawa ta daka
ma Beeba kee mai kikeyi a gunsu, kin
dawo ko sanar ni bazakiyi ba, ni bana
son kina taraya da mai fiska kaman na
muciya.
Oh! Ni Rash nace”wannan
Gwaggon wata irin macece ta fiye son
kanta, anya ma idonta na gani kuwa?.
Duk irin kyan Khadi tana zaginta.
Ko beeba ma bazata gwada mata kyau
ba don ta d’aran mata nesa ba kusa ba.
Taku a kullum mai k’aumarku .
ﺭﺍﺷﻴﺪ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺔﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-16~20.
Jiki ba kwari Beeba ta nufi d’akin, don
sam ita bata son irin yadda mahaifiyarta
ke nuna tsana ma Khadi. Gash’i ko
kad’an Khadi bata nuna damuwarta
kuma hakan ba sh’i zai hanata biyayya
ba.Allah yasa Gwaggo ta gane. Ya sh’irya
mana ita Ameen.
‘Dakin su tash’iga Gwaggo ta
balbaleta da masifa, Gwaggo tace”Beeba
bana son ganin ki da wancan mai
fuskan mujiyan, kema kuma sai niman
kai kike da su. Ni har Malam da ke biye
mata ba kyalesh’i zanyi ba, ko kad’an
bana k’aunar in bud’e ido imganta a
gidan nan.
Beeba tace”haba Gwaggo ba kyau
fad’an haka fa, kuma ae Addah tana iya
k’ok’arinta gurin kyautata miki. Ita ne
kulum cikin aiki bata hutawa ko ni bana
miki aikin da take, nikam ina son Addah
na tana da halaye mai… Bakinta Gwaggo
ta make tare da wata harara tace”kee a
kul d’inki kar na kara jin cewa kina
had’a kanki da wannan yarinya, Ko
kema ta shanye miki Zuciyan ne?, kama
yanda ta shanye na Malam baya ganin
laifita baya son amata fad’a.
Beeba tace”ko d’aya Gwaggo gsky
kenan Khadi tana da halaye mai kyau.
Mts Gwaggo ta ja tsaki ga abinki can
maza ki ci don zaki gidan Innan ku, zaki
anso min aika a gunta. Beeba ta d’auko
abinci zatafita gunsu Malam Gwaggo ta
dakatar da ita, ba yanda ta iya dole yasa
taci a d’aki badan taso ba, don ta fi jin
dad’in kasancewa da yar’uwanta.
Gwaggo tace”Beeba yi sauri ki
sh’irya kije min gidan Inna ku. To ta
amsa ta kammala cin abinci tayi wanka
ta d’auko kayanta masu kyau ta sanya
su, ra fes da ita. Gwaggo “nagama sh’irin
ke nake jira kizo fad’an sakon, don inje
kar dare ta min a hanya.
Sai da Gwaggo ta d’auko sakon da
zata kai ma Inna kafin ta bata kud’in
mash’in tace”kice ta had’a miki duka
aikan harda kayan da na saya d’in, to ta
amsa ta fito sai da tayi sallama wasu
Malam kafin ta tafi.
Taku a kullum mai k’aunarku
ﺭﺍﺷﻴﺪ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Notice
Masu karatu na zansa sunan
littafina daga KHADEEJATUL-KUBRAH
zuwa YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU,
cos Daman YAR’RIKO ne suna Da na fara
sawa, sai aka samu wacce tayi. So yanzu
namar dashi YA’YA DA DUKIYA BA’A
K’ETARSU. Yafi ma’ana kuma sakon
littafin akan haka zai tafi.
Pg-26~30.
Ana kiran sallah tayi d’akin su ta
kwanta, kasanewan garin da sanyi
lokacin hunturu ne. Addu’a tayi ta
kwanta ga yunwar da ke addabarta.
Haka har bacci b’arawo yayi awon gaba
da ita.
Dukun-kune take a yar ta barmata gefe
kuma katifar Beeba ne yar k’arama
wanda mutum d’aya zai d’auka. Bacci
take amma sanyi ya dameta. Kiran
Sallah asuba ya farkar da ita da kyar ta
mik’e ta d’ibo ruwa a randa sai d’ari
take yi. Alwala tayi ta koma d’aki tayi
sallah bayan ta idar ta fara azkar d’in
safiya wani bacci ne ya d’auketa kamar
daga sama taji an shek’a mata ruwa mai
sanyi nan take ta fara d’ari-d’ari, duk da
haka Gwaggo bata kyaleta ba wani
ruwan ta k’ara kwara mata. Barin da
takeyi ya tsananta, Gwaggo tace”ke har
kimsami daman da zaki kwanta bacin
safe, uban wa ya baki dama?.
Malam yana karatun Al-qur’ani mai
girma sai yaji kamar ana hayaniya jin
maganan yayi yawa ya fito, yaji d’akin
su Khadi ne da sauri ya sa kai cikin
d’akin ganin Khadi ta fi luuuu zata fad’i
yaje da sauri yana”Salati ya tare ta fad’a
a hannunsa cikin k’unan rai ya d’ago ya
kalli Gwaggo yace” in kin kasheta ae kin
huta, kin san yarinya tana fama da
Pneumonia kuma yayi mata yawa zaki
kwara mata ruwan sanyi, haba hauwa
anya kina tsoron Allah kuwa ae d’a ko
ba kai ka haifeshi ba, bai kamata kina
wula kanta ta ba.( Yan uwa mata kira
gareku, kune jigon gida duk lokacin da
gida yayi kyau kune, kusani Ya’ya da
Dukiya, da Dabba ba’a mugun tar su. A
rauwa ba kasan wanda zai taimake ba,
sai kaga d’an da ka haifa da cikin ka
wani lokacin bai jik’anka ba, wanda
baka san zafin sa ba ya taimake ka
kuma Ya’ya Rahmane dan Allah kuna
kyautata ma yara ba sai naka ba ku
d’auka duk d’aya suke a gunku).
Gwaggo ko a jikinta tayi waje tana
cewa”ni dai dole ta fito ta min aiki yau
ko ta ji a jikinta. Malam ya kali Khadi ta
idanunta suka kafe a sama da sauri ya
d’auketa ya fita waje da ita. Beba da ta
fito daga d’aki ganin halinda Adda ta ke
ciki yasa tayi gun Malam da hanzari
suka fita dake garin da sanyi da kyar
suka samu mai Napep yace”Yaro Asibitin
Murtala zaka kai mu, Malam da Beeba
suka shigar da ita ciki suka d’au hanyar
Asibitñ, sun d’anyi tafiya kafin suka iso
asibitin, kud’in mai napep ya basa kafin
ya d’auki Khadi suka shiga cikin Asibitin
nurse suna hango su, suka tahoda sauri
suka karb’eta. Emergency aka nufa da
ita, Dr Abdul ke bakin aiki, da sauri
“nurse suka sanar masa an kawo patient.
Yace “ok! I’m coming now”.
Bata dad’e da isa gun su Malam sai ga Dr
Abdul nan ya iso. Dubata ya soma yi
yaga tana wani yanayi numfashinta na
shirin d’aukewa, tai makon gaggawa aka
bata cikin ikon Allah suka samu
numfashinta ya dai-daita. Magunguna ya
rubuta ya mika wa Malam yace”Baba
gashi kaje Pharmacy ka sayo, in ka dawo
ka bawa nurse sai ka same ni a office
d’ina. Malam ya amsa da rawar jiki ya
nufi pharmacy.
Taku a kulum mai k’aunar ku .
ﺭﺍﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-21~25.
Malam suna hira da Khadi Gwaggo ta
fito wani sak’on kalon da Gwaggo ta
aika ma Khadi, yasa ta mike ba sh’iri ta
nufi kitchen ta d’aura girkin dare, sai da
ta magama aiki Gwaggo tazo ta d’auke
tukunyan d’akinta ta sh’iga dash’i duk
abun da suke Malam na kalon su bai ce
mata komai ba. A zuciyansa ya na mai
jin-jina bak’in hali irin na Gwaggo,
Malam ya mike ya fita waje zuwa gurin
da suke d’aukan karatu.
Rabi ce ta sh’igo tayi d’akinsu ta
nufa ta dau naira goman Gwaggo tasa a
wando ta fita waje, alawa ta siya sai da
ta shanye kafin ta dawo gida.
Gwaggo tazo d’aukan raina gomanta don
a siyo mata sikari ta saka a surki, taga
babu kud’i cike da masifa tazo ta danki
Khadi tace”ke barauniya bani kud’i na
da kika d’aukar min wato satan ma
gadonsa kikayi a gun uwar ki.
Khadi tace”Gwaggo ko d’akin ma
ban sh’iga ba ina zaune a nan gurin fa.
Gwaggo tace”oh! Sharri zan miki ko?. Ni
a ya’ya na babu b’arawo ba mu gaji sata
ba sai dai ko gun uwarki ne zuri’an
barayi. Nan take Khadi ta soma hawaye
jin takaicin yanda ake kiran iyayenta da
suke kasa.
Eyeh lalle kin samu gu dan ban
dakaki ba shine kike kuka ko?. Gwaggo
ta d’auko dorina tazane Khadi sai da taji
hannu ta ya gaji tace”naira goman da
kika d’auka a madadin abinciki na yau
da kuma karin safiya. Gwaggo ta juya
zata tafi sai ta dawo ta rike kunne Khadi
tace”saura in Malam ya baki abunci ki
karb’a ki gani ni dake yau a gidan nan.
Ina son ana kiran Sallah ki sh’iga d’aki
ban yarda ki leko waje ba, ina ga
munanan kafarki a guri kin san sauran
ta nufi d’aki.
Taku a kullum mai k’aunar ku
ﺭﺷﻴﺪ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-31~35.
Malam ya sayi maganin dubu buyu da
d’ari biyar ya nufo k’ofan Emergency ya
mika ma nurse “Malam ya tambayi
office d’in Dr Abdul nurse ce ta gwada
masa, godiya ya mata nufi office d’in, da
Sallaman sa ya tura k’ofar aka bashi
izinin shigowa, Dr ya nuna masa gun
zama Malam ya zauna. Sai da Dr ya
gama yan rubuce-rubucen sa tukun ya
d’ago da fuskansa tare da zare yar faran
glass d’in da ke manne a kyakyawan
fuskansa. Malam ya msa sannu da
aiki,Cikin girmamawa ya amsa, kali
Malam yace”Baba jikin Khadeeja yayi
tsanani sosai, mai yasa kuke barinta
tana aiki da ruwan sanyi?, kuma tana
zama a inda ke da sanyi, mai ya kawo
hakan bacin na sha fad’a muku illar
hakan amma kun kasa koyayewa. Malam
da jikinsa yayi sanyi yace”Dr in Allah ya
yarda wanan karon zamu kiyaye fatan
mu kawai yanzu ta samu lfy. Dr Abdul
ya kallesa sosai tabbas ya gano damuwa
a cikin idonsa ga alamar magana a
bakinsa, amma tunda bai fad’a ba “ni
dai zanyi iya kokarina ganin na taimaka
mata, ya Allah kabata lfy ameen. Ya kalli
Malam yace”shikenan zaka iya tafiya
amma akula mata da shan magani. Kai
Malam ya d’aga masa alamar eh!. ‘Dakin
da aka kwantar ta ya yashiga Beeba ya
gani a bakin gadon ta zuba mata ido ga
alamar tayi kuka sosai. Da Sallama ya
shigo Beeba ta masa sannu ya amsa tare
da zama a d’aya daga cikin plastic chairs
d’in dake d’akin. Yace”Beeba ya jikin
Addah ki?. tace” da sauki amma har
yanzu bata tashi ba, bacci take ya kalli
Khadi yace”Allah ya baki lfy, cikin
zuciyar shi kuwa cewa yake” ya zama
dole in d’auki mata ki akan Gwaggo
bazai yiwu Khadi taci gaba da wahala
haka ba. Ya mike ya nufi k’ofar Asibiti
ya sayo musu abinci ya dawo ya kawo
musu nan Beeba ta karya, shima sama-
sama yaci abincin.
Gwaggo ne tafito daga bayi ta na
zuwa d’aki taga ba Beeba ta duba d’akin
su Khadi taga bata nan d’akin Malam ma
baya nan, Rabi ta tambaya tace”kee ina
Beebalo?. Rabi ta kalli ina tace” ba sun
fita da Malam ba naga ya riko Adda
Khadi, tsaki tayi ta leko titi basa nan,
nan takama bala’i yau zaizo ya sameta
akan me zai fita mata da yarta don wata
marar galihu, ita yarta na galihu, cikin
gida ta koma sai surutu take ita d’aya.
WACECE KHADIJA?.
khadijatu~Kubrah shine asalin sunan
Khadi ya d’aya tilo ga Malam Adam.
Malam Adam haifafen garin kano cikin
unguwan Dakata gurin fire service.
Yayan Malam Ahmad ne Ubansu d’aya
ne. Tun Malam Ahmad na karami Allah
yayi rasuwa Mahaifiyar sa, ya koma
hannun Maman Adam wato Kakan Khadi
kenan, ta yi musu rikon tsakani da Allah
har suka girma. Adam shiya fara yin
Aure kasan cewan shine babba sun
shekara da yawa da matar sa Balkisu
Allah bai basu haihuwa ba, sai daga
baya ta samu ciki ya zo mata da laulayi
haka tayi ta fama har tazo haihuwa, ta
kwana biyi tana na kuda, kafin rannan
ukun har ana shirin shiga da ita
operation ta haihu ko juyawa batayi ba
Allah ya karbi abunsa. Malam Adam yayi
kukan rashin matarsa mai hankali da
kirki, watan ta shida da rasuwa Baba
Ahmad yayi Aure, ya auri matar sa
Hauwa amma auren dangi sukayi yar
kwan war Maman sa ne,(danganta karsu
ta gun uwa kenan da haiwa). Hauwa
macece mai masifa tun tana budurwa ta
ki jinin Balkisu Maman Khadi ganin
yanda Ahmad ke zama a d’akinta hakan
yana bata haushi sosai.
Cikin ikon Allah Khadi ta samu kulawa
in ka ganta bazaka ce bata sha nono ba
madara take sha bul-bul da ita ga ta da
gashi ga kyau sosai, gwanin burgewa.
Hauwa shekaranta 3 da Aure ta haifi
yarta Beeba kar kuso kuga murna gunta,
ta d’au son duniya ta d’aura ma Beeba,
ta taso cikin kulawa ga hankali, in ka
ganta sak Malam Ahmad kamar kakinta
yayi, yarinya mai hankali da nutsuwa,
jinin su ya had’u da Khadi tun Beeba na
karama Khadi ke mata wasa komai ta
samu zata kawo mata, amma in Gwaggo
ta gani ta kwace ta yar ta daki Khadi,
ana cikin haka wata ranan talata Malam
Adam ya tashi da ciwon Ajali kwanasa
biyar Allah ya karbi abunsa tun daga
wannan rana Khadi ta dawo hannun
Malam Ahmad da zama, nan Gwaggo ta
samu daman galla za mata, sam bata
kaunar ganin Khadi da Beeba sun zauna
gu d’aya.
ﺭﺍﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-36~40.
Sam Gwaggo bata ‘kaunar ganin Khadik,
da Beeba sun zauna gu d’aya. A kwai
wani rana, da Khadi na wasa ma Beeba,
Gwaggo na zuwa ta saka k’afarta ta
shure Khadi, ta fad’i akan hannu ta, sai
da ta gurd’e. Ranan ran Malam ba
‘karamin b’aci yayi ba, har sai da ya
mari Gwaggo. Tun daga lokacin ta ‘kara
tsanar Khadi, har zuwa girmanta, sam
bata tausaya mata, duk aikin gidan
Khadi keyi, Beeba kuwa bata son ganin
Khadi cikin damuwa, in Gwaggo ta bata
ma Khadi aiki, sai ta faki idon Gwaggo
ta zo ta tayata su gama. Haka rayuwansu
ya kasance dad’i da ba dad’i, Malam ya
sanya su a Makaranta Khadi da Beeba
suna ‘ko’kari, amma Rabee kam in ban
da niman tsokana ba abunda take. A
hakan har Khadi ta kammala Secondary
school d’inta, ta barsu Beeba yanzu ke
karatu har islamiya an yaye ta. Matsalar
ta d’aya ne sam bata kula saurayi, ko
sunzo Gwaggo koran kare take musu, wai
baa su nimi mayya ba. Tana lashe
zuciyar mutane, har ta lashe na Malam
da yarta Beeba. Hakan sam bai damun
Khadi,ita kulum da Malam addu’a su,
Allah ya shiryi Gwaggo yasa ta gane.
Wankin Gwaggo dana Ya’yanta Khadi ke
yi, in tafara sai ta gama, bata isa tace”ta
gaji ba Gwaggo zata fara mata bala’i,
wani lokacin, abimci ma hana ta take.
Back to lbr.
Khadi bata farka ba, sai kusan k’arfe sha
biyu, sai da Malam ya ga tasamu ta ci
abinci, kafin ya musu sallama, akan
zaije shi gd ya dawo, Beeba ta mishi
adawo lfy, ya fita.
Yana isa gd, Gwaggo ta taso cikin
masifa, tana tambayar sa ina ya kai
mata yarta?. Ko dun bai damu da ita ba
ne, yana son wannan mayyar ta lashe
mata kurwa, kamar yarda uwarta ta
lashe zuciyan mutane. Sai da ta gama
sababinta Malam bai bi ta kanta ba,
abincin sa ya d’auka, ya fita tare da
tabarma da pillow. Gwaggo na ganin ya
fita, gyale ta d’auko ta fara binsa a baya,
har taga ya nufi Asibitin Murtala, itama
tace”ma me Napep su bi Malam, haka ko
akayi, har ya shiga cikin asibitin, ta bisa
a baya, har ‘kofan Ward d’in da aka
kwantar da Khadi. Ta na labe taga ya
shiga d’akin bai dad’e ba ya fito, ya nufi
wani guri a cikin asibitin. ta na shiga,
gadajen ta rink’a bi, har ta iso na su
Khadi, wani mugun kalo ta sakar ma
Khadi,da ke jin gine da pillow,
tace”mayya kin lashe zuciyar mijina da
yata, to bakiyi sa’a ba, tana zuwa kusa
da ita, ta wanke ta da kyakyawan mari,
nan take yan d’akin suka yi mata caaa.
Kafin ka ce me, guri ya d’auka da
hayaniya. Dr Abdul ne ya fito daga Ward
d’in dake, kusa da na su Khadi,
hannunsa rike da waya, da alamar waya
yakeyi. A hankali ya ke tafiya, tun daga
nesa ya ke jin hayaniya, yace”Dr Umar
ina zuwa, naga kamar female ward na
lfy, bai karasa ba ya iso gun hayaniya,
yayi yawa, da kyar ya kutsa zuwa cikin
gun, sam ya manta bai kashe wayar ba.
Dr Umar shima bai kashe ba, dai-dai
lokacin Malam ya iso gurin, ganin
abunda ke faruwa ya soma jan Gwaggo
da ta rufe Khadi da duka, sai zuba
bala’in take. Dr Abdul ya iso yana “tan
bayan lfy?. Gwaggo sai wani fin cikewa
take, Malam ya d’auke ta da mari. Ta
d’ago tana kalon Malam tace”ka mare ni
a kan wannan banzan, mayyan mai
kod’ade’en fuska. Ba zan yarda ba, sai
na rama ta sake yin kan Khadi, itakam
in banda kuka ita da Beeba sun rike
juna. Dr Umar da ke jin duk abunda ya
faro, duk da baya gurin amma ransa ya
baci sosai, cikin zuciyarsa yace”duk da
bansan maike faruwa ba amma wata
irin macece haka?. Malam ya ransa ya
baci mari ya sake wanke Gwaggo da shi,
zafin yasa ta nutsu sosai, sai ta dawo ta
fara jan Beeba, ita ko gadon ta rike,
security aka kira suka fita da ita. Sai da
guri ya lafa, Dr Abdul yace”Baba ka
sameni a office d’ina ya fita, Malam ya
nufi office d’in sa.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-41~45.
Sai da guri ya lafa,Dr Abdul yace”Baba
ka same ni, a office d’ina. Biyosa yayi,
suka nufi office d’insa. Sai da Dr ya
zauna, yace”Baba ka zauna, magana
zamuyi da kai. Malam ya zauna, ya na
fiskantan Dr, gurin shiru kusan, na minti
biyu, kafin Dr ya nisa yace”Baba ina son
in tan bayeka ne game da Khadija.miye
alakarta da wannan matar? Kusan
yawanci lokuta, in kun kawo Khadija ba
ta da lafiya, matan nan sai ta mata abun
da zai kunta ta. anya kuwa mahaifiyarta
ce?. Malam ya nisa yace”gaskiya ba
mahaifiyarta bane, Khadija yar riko ne a
hannu mu, nan Malam ya kwashe
tarihin Khadi, ya basa a takai ce, ba Dr
Abdul ba, ni kaina Rash na tausaya
mata.wayar sane tayi haske alamar kira
ya yanke, d’agawa yayi, ya ga duration
wajan awa d’aya da rabi, sai alokacin ya
manta, bai kashe wayar ba. Dr Umar da
ke jin, duk abun da ya faru da Khadi,
tare da tarihin rayuwan ta, take yaji
yana son tai maka mata. Ta bashi
tausayi, da ace yana 9ja da ya san
abunyi, kwanciya yayi, a lafiyayen
gadon sa, fiskansa yana kalon silin, cike
da tunani kala-kala, har bacci ya
d’aukesa.
Dr Abdul ya nisa yace”gsky Baba ya
kamata ka d’au mataki, don yarinyan
nan, tana yawan aiki da ruwa, ga
wahala ya mata yawa. Malam
yace”nagode in Allah ya yarda, zan d’au
mataki, sallama ya masa ya koma, gunsu
Khadi da har a lokacin, kuka takeyi
sosai, ko da ya iso, ya kalleta cike da
tausayawa, yace”Khadeejatu~Kubrah!, ki
kara hak’uri akan na da, nasan ki mai
biyyace, duk da Gwaggo tana cutar da
ke, kuma kina hak’uri, ki ‘kara akan na
da, kinji ‘yar albarka, kai ta d’aga masa
alamar eh!. Sanna tace”Baba ka maida
Beeba gida, tunda Gwaggi bata son
zamanta anan. Murmushi yayi,
yace”Beeba ba inda zata koma, har sai
an sallame ki, Beeba ‘yatace nafi,
Gwaggon ku iko akanta. Nan ya ta gaya
mata kalamai masu dad’i, har ta mance
da muwarta, dariya suke yi, ita da
Beeban ta.
Gwaggo ko da ta koma gida, taringa
masifa da zage-zage, har Malam ya dawo
bata daina ba, har tana cewa”kasake ni
mana, tunda yarinyan ta lashe
kurwanka, d’aki ya shiga, ya kyaleta ta
gama sababinta.
Kwanan su Khadi biyar, a cikin Asibiti
aka sallame su, tun a hanya take far
gaban, dawowa gida, don bata san dame,
Gwaggo zata tareta ba.
Dr Umar kuwa tunda yaji labarin,Khadi
yaji yana son tai maka mata, yarinyan
ta bashi tausayi. Wayarsa ya d’auka ya
kira Dr Abdul bayan sun gaisa yace”ya
aikin dai? Daga ban garen Abdul
yace”Alhamdulilah! Aiki ba dad’i. hira
sukayi sosai, Dr Abdul yake tambayar Dr
Umar yaushe zaka kare course d’in nan?.
Ajiyar zuciya yayi, kafin yace”saura
wata shida mu gama, nima na damu in
dawo 9ja, nayi missing abubuwa da
yawa. Cikin zolaya Dr Abdul yace” harda
Baby Sakina ko?. Mtss yayi d’an tsaki
yace” ana ta kai, waya ke ta kaya.
wannan mayyar yarinya, maras kamun
kan, ina zan kaita?. Ae saninta ya fi
nawa. Yauwa ranan wacece naji ana
hayaniya akanta?. Rannan muna waya
da kai, kamar a Ward d’in mata ne, sai
da Dr Abdul ya d’anyi tunani kafin
yace”ok! Khadijat ne, nan ya kwashe,
labarinta ya basa. Dr Umar ba karamin
tausaya mata yayi ba. Ya kuma kudiri
aniyar, duk randa ya ganta cikin
damuwa sai ya tai maka mata, duk da
bai san ya kamani ta yake ba.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-46~50
Suna isowa gida, Beeba ta ba wa mai
Napep kud’insa, ta d’auko su bargo, da
pillow, suka nufi k’ofar shiga gidan.
Khadi ta tsaya, Beebah ta juyo ta kali
Khadi, Tace”lafiya naga kin tsaya?. Nan
take idon Khadi ya kawo ruwan hawaye,
tafara magana, cikin muryan
kuka,”Beebah ina tsoron shiga cikin
gida, don Gwaggo zata iya dukana, kinga
Baba baya nan, Beeba ta kalleta cike da
tausayawa, Tace”Addah muyi addu’a in
Allah ya yarda bazata yi mana komai ba.
Kalamai masu dad’i, da ‘kwantar da
hankali, tayita fad’a ma Khadi, kafin ta
yarda sukayi addu’a, tare da shiga gidan.
Assalamu’alaikum! Gwaggo dake d’aki,
tanata sababi, taji kamar muryan Beeba
da sauri ta fito, har tana tuntube, tana
fitowa taga su Khadi, wani uwar ashar ta
narka mata, da kalon yau zaki sani.
‘Daki ta koma, ta d’auko wata
zu’ke’kiyar bulalan ta, Gwaggo tace” yau
sai na rama, marin da kikasa Malam
yamin, kuma wahala yanzu kika fara,
Mayya kawai, sam tsabar bala’i, bata
lura da qofar window, dake bud’e ba,
jikake Garamm Gwaggo ta gwaru da
window, sai da ta fadi a kasa. Nan take,
ta saki ‘kara, oh ni Rash nace”su Gwaggo
ko d’an dauriya babu. Ihu take kamar
qaramar yarinya, Khadi da gudu, ta iso
gunta fiskanta, d’auke da hawaye, sannu
take ma Gwaggo, cikin tausayawa.
Gwaggo da ‘kyar, ta iya yin shiru, tana
d’agowa kuwa, bakin ya kumbura
sundum, ko danaga bakin, bansan
likacin da nasaki dariya ba. Gwaggo
d’aki tayi, ko magana bata iyayi, sabida
bakinta, paracetamol ta sha, don ta ji
sanyi ajikinta. Khadi kam d’aki ta shiga,
ta takure gu d’aya. Tana cike da tunani,
mai tasa Gwaggo ta tsane ta haka?. To
mai iyayenta sukayi ma Gwaggo ta ke
tsanar su haka, har ya shafeta?. Duk
wayannan tambayan bata da amsansu,
haka ta hak’ura, dan bata da amsan
tambayanta.
Gwaggo tunda baki ya d’anyi sau’ki, ta
soma gana ma Khadi azaba, na yau
daban, na gobe daban, wani saran da ta
samu, in Malam nanan, bata cika gallaza
mata ba, amma in Malam ya fita, Khadi
sai ta gwammace kid’a da karatu. Khadi
ta yanke shawaran samun Malam,
Tace”Baba ina son, in fara zuwa gurin,
koyan d’inki, yafi zaman da nakeyi.
Malam ba k’aramin dad’i yaji ba, kuma
hakan zai ragemata, yawan damuwa,
sati guda ya nima mata, tafara zuwa,
amma sai dai yana nesa da unguwansu.
Gwaggo tayi bala’i ba ‘kadan ba, gani
bata da mafita yasa ta hak’ura, tafara
tunanin, sabon hanyan da zata, gallaza
ma Khadi.
Kwanaki sun tafi,Yau saura sati d’aya,
Dr Umar ya kammala course d’insa, suna
yawan waya da Dr Abdul.
Khadi tana zuwa gurin k’oyan d’inkinta,
gata da hazaka da basira, yanzu har ta
fara had’a kayan yara, zata yanka da
kanta ta had’a. Ganin haka yasa Malam
ya sayo mata, keken d’inkin hanu,
dontana, yan facin da sanda na mutane,
tana samun biyar goma. Masu karatu
karkuso kuga Gwaggo ranan, kamar
zatayi hauka, dan bak’in ciki da takaici,
Khadi kam kule kanta, tayi a d’aki, don
Gwaggo tace yau ko ita ko Khadi.
Fanz kumin hak’uri, na rashin jina,
k’wana biyu, bama samun wuta ne.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-51~55.
Gwaggo tun da taga Khadi, tana d’an
samu a d’inki, hankalinta ya tashi,
Gwaggo ta kudiri aniyar sai ta b’ata
keken d’inkin. Beeba ko murna ganin
Addah ta, tasoma iya d’inki yanzu zata
bar kai d’inki, ana wulakanta ta, Gwaggo
ko kulum sai ta zagi Beeba, akan yanda
take, nuna zakewar ta ga Khadi. Haka
rayuwa tayi ta tafiya, Khadi na cikin
kunci da matsin Gwaggo, hak’uri takeyi
da ita, kulum sai taci kuka, yanda
Gwaggo ke zagin iyayenta.Yanzu har ta
kai, yan’unguwa sunsan, Khadi yar riko
ne a hannusu. In Gwaggo taga Malam
baya gida ta hana Khadi zuwa gun
d’inki, in makwabta sun kawo faci,
Gwaggo ta korasu, ta hana su shiga cikin
gidan. Khadi kusan sati bataje, gun
koyar d’inki ba. Malam baya samun
zaman gida, sabga sun masa yawa, gashi
yau tafiya ta kamasa zuwa Jigawa, tunda
asuba yatafi. Zaije ya sayar da Gona’nsa
dake garin, don fara sayyan auren
Khadi. Da wuri ta tashi tayi wanke-
wanke’nta gama, ko karyawa batayiba ta
d’au hijab da nikaf d’inta, ta fito cikin
sand’a, takalmanta a hannu ta rike dan
Gwaggi kartajita, cikin sand’ a ta fita, a
qofar gida ta sanya hijab dinta. Sauri-
sauri ta fara tafiya sai da tayi nisa ta
duba jakanta, taga naira d’ari ya rage
mata, Gwaggo duk ta amshe sauran
kud’in. Mai Napep ta tsara, ta masa
k’watancen gurin, Yace”tabada naira
d’ari, nan tafara “rok’ansa ragi, da kyar
ya yarda zai kaita a naira Saba’in. Ta
shiga suka d’au hanya, ko da taje sai da
mai koyamusu d’inki, ta mata fad’an
rashin zuwanta, hak’uri ta bata.nan suka
fara aiki har sai da karfe hudu suka
tashi, din yau sun samu K’wangilan
dinka uniform d’in wani school.
Dr Umar ne ke waya, yana sanar da
Mum d’insa zai da wo 9ja, girki na
musamman Ummin sa ta masa, ko da
jirginsu ta iso, driver ne da kanwarsa
Iham sukaje d’auko sa. A hanya suke
hira da ilham, yana tambayar ta,
yan’uwa da abokan arziki, har suka iso
gida, tun daga nesa nake hango securitys
a qofar gidan, tabbas ko ba’a fad’amin
ba, Umar d’an wani babban attajiri ne,
ko mai mulki, don masu karatu, bazan
iya tsara muku kyan gidan ba. Tundaga
gate masu aiki, ke masa sannu da
dawowa, har ya isa cikin wani falo, niko
Rash ganin irin kyan gidan nace”bazan
bari a bani labarin cikin gidan ba, da
hanzari na sanya kaina cikin falo,
yasalam masu karatu hmm wai in bakayi
bamu guri, karkuso kuga cikin falon,
sannu a hankali, nafara bin falon da
kalo, komai na golden da brown ne, ko
dana d’aga kaina wasu koyaye ne
tamkar zinari, sai haskawa sukeyi a
cikin falo. Gefe na samu na rab’e don
yanda sanyin A.C ke bugani, ga wani
sassayan kamshin da ke tashi, wata yar
datijuwa ce, ta fito d’auke da fara’a,
afuskan ta ta iso cikin falon, tana
cewa”ur welcome my son. Cikin
girmamawa yaje yayi hugging d’inta,
yana fad’i” i miss u too my lovely mum.
Kanshi ta shafa, tare da rike hannusa,
my Son “muje ka watsa ruwa sai kazo ka
ci abinci ka huta. Mikewa yayi ya nufi
side d’insa, komai a canza masa na
d’akin, wanka ya shiga, bayan ya fito ne
ya nufi falo, nan ya cika cikinsa da
abinci kala-kala, yana kammalawa
kenan ya nufo falo, wani daga cikin
security d’in yazo, yace”Oga kana tare
da bako Dr Abdul, ya kalesa cikin
girmamawa, Yace” barshi ya shigo ae ba
bako bane shi d’an gida ne. Dr Abdul ne
ya shigo, sai da ya gaida Ummin su Dr
Umar, tukuna suka nufi side d’in sa, hira
sukayi sosai kafin ya masa sallama, akan
zasu had’u, sai da ya rakosa, har jikin
motarsa yashiga sai da, Dr Abdul ya bar
gidan, kafin ya koma cikin gida.
Amin afuwa, har yanzu wuta bai tsaya
ba, shiyasa kuke jina shiru.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-56~60.
Yau kwanan Dr Umar 8 da dawowa, har
ya koma bakin aikinsa, tun safe yake jin
son yawo zai zaga gari, kuma bai son
security ko d’aya yabisa, don shi daman
bai cika fita da security’s ba, don Dad ke
matsa masa baya son yana yawo haka,
ko driver yana bari yana jansa, yana
tashi a office karfe 3:30pm, gida ya nufa
yayi wanka, yau sai ya tsinci kansa da
son sanya jamfa, nan ya ciro wata
shadda dark blue amata aiki, da surkin
farin zare da blue, hularsa ma blue ce da
surkin fari, ya d’auko ta kalminsa ya
tare da agogo, tsayawa yayi a madubi,
yana kare ma kansa kalo, gaskiya ya
hadu ko ni Rash dana kalesa, sai da
kirjina ya bada dumm, Umar mutum ne
mai kyau ga kamala ga k’warjini, fari ne
tass, yana da dogon hacci tare da
karamin baki, kai in ka kallesa sai
karasa da wani yare zaka danganta shi,
India ne ko balarabe, ko Fulani. Tunda
ya sauk’o falo falo, umma ta ga d’anta,
sai murmushi take zubawa, tace”Baba
na sai ina haka?. “Wananan wankan fa?.
“Ko nayi surkace?. Don raboka da saka
manyan kaya ka dade. Cike da
murmushi ya kalli Umma, Yace”
Ummana duk wannan tambayar ni
kad’ai, bata surka Umma da saura tukun,
zan dai zaga cikin gari ne. Cike da
kulawa tace”Allah yasa futanka a
samomin surka mai hankali da tarbiya,
yar mutunci, cikin jin dad’i ya amsa da
Ameen. Tace”Son Allah tsare a dawo
lafiya, ka kuma tafi a hankali, to ya
amsa ya fita, tun a harabar gidan
ma’aikata ke masa sannu kud’i ya ciro a
aljuhunsa wanda bai san nawa bane ya
basu, ya shiga motarsa ya ja.
Khadi tafe take, tana tunani yau ta
kad’e, in cikin zuciyar ta tace” yau gashi
malam baya nan, nikam na banu,
bansan wani irin duka zata min ba. Hala
yau kamma, k’wananane ya kare, nan
tafara “Ya Allah ka yafe min, kasa na
cika da imani, wasu hawaye ke bin
fuskarta. Tafiya take sam bata san inda
take nufa ba. Tsaban zance zuci, har ta
hau kan titi, jama’ a dake hanyar sai
kalonta suke, wasu na tausaya mata,
gashi fuskanta da nikaf, jama’a na ta
mata magana sam bata sani ba, bata ma
san sunanyi ba,”wai kunu a wani gida”.
Dr Umar na tafe a cikin motarsa, ya
kuna qira’ar Ahmad Sulaiman, yana tafe
cikin nutsuwa, ya wuce ran about baban
gwari kenan ya d’auki hanya. Sam bai
hangi yarinya ba, sai da yazo kusa ya
ganta. Sai tafiya take a tsakiyar titi ga
mutane sai kalota suke horn yayeyi da
k’arfi, amma sam bata ji, gashi ya d’au
gudu sosai, wani wawan burki da yata
kane yasa dawo cikin hayyacinta, damar
motan, ta gabanta ya tazo, suman tsaye
tayi, dan tsaban razana ita bata fadi ba
ita bata motsaba.
Da sauri ya fito cikin motar, yana zuwa
kusa da ita, yaga bata motsa ba ga idonta
sun kafe, cikin dakiyar zuciya yave” ke
lafiyarki klau kuwa kika hau kan titi?.
Me kike tunani haka? Luuu yaga ta tafi
zata fad’i cikin zafin nama ya tareta, ta
sauka a jikinsa. Jijigata yayi yaga bata
motsi, cikin sauri ya fincike nikaf dinta,
sam bai ga fuskanta ba, juyaa yayi, ya
kali wanda suka taru a gun, wasu na
masa kalon mamaki, wani d’an tsoho
yagani yace”Baba pls kazo ka taimaka
min dan Allah. kamata sukayi, suka
dawo da ita gefen titi, da sauri Dr Umar
yaje da gudu ya bud’e motarsa, ya
d’auko goran ruwa, yazo ya yayya fa
mata, sai a lokacin ya kali fuskan, kasa
d’auke idonsa yayi, yana furta”Sarki ya
tabbbata ga ubangijin sammai da kassai,
lalle ubangiji yayi hallita a gurin. a
hankali tasoma bud’e idonta, tarass ta
sauke su akan, Dr Umar da ya zuba mata
na mujiya, ya kasa d’auke kansa ga
fiskanta.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-66~70.
Gwaggo cikin hayaniya da masifa,
Tace”mai yasa baka tura, Beebah ko
Rabee’atu, sai Khadi, to sai dai na k’ona
kayan. Malam kasa magana yayi, tsaban
takaicin dake damunsa, wannan wace
irin fitinaniyar macece?. Gwaggo ta d’ibi
kayan, tayi hanyan kitchen dasu, Malam
na ganin haka ya bita, kafin ya isa, har
ta fara sawa a wuta, kwacewa yayi tare
da zaro na wutan, wani gyalens mai
kyau, da sauri ya taka, da takalmin sa,
wutar ta mutu. Wani gumun kalo ya
mata, duk iskancinta sai da ta shiga
taitayinta, ta fito a kitchen, koda tazo
dai-dai gun Khadi shureta tayi da kafa,
sai da Khadi ta fad’i, ta Beeba ne ta
d’aga ta, rana mata sannu, Malam
yace”Hauwa mai yasa baki da tausayi
ne?. Kina tuna kema zaki mutu kuwa?.
Ki sani fa duk inda, iyayen Khadeeja
sukaje, kema zakije, kuma Allah baya
kyaleki bane, kuma nima ba wai fa
tsoronki nake ji ba, ina d’aga miki k’afa
ne. Hauwa kisani ‘YA’YA DA DABBA, DA
DUKIYA, BA’A K’ETAR SU, bakisan wacce
irin baiwa Allah yayi ma Khadija ba,
bakisana wani irin taimako, zata miki a
rayuwan ki nan gaba. Gwaggo ta kali
Malam cikin kalon da ban d’au maganar
ka da muhimmanci ba, tace” ehehehe
Khadi ne zata taimaken, ahir ahir, Allah
ya tsare gatari da saran k’ota, ni da
Khadi badai muzauna inwa d’aya ba.
Malam ya kaleta yace”Hauwa da badun
Allah bayason saki ba, to da yau tabbas
sai kin bar gidana, kuma kinci
albarkacin Khadi da ‘YA’AYAN da kika
haifa. Koda Malam ya ambaci saki, sai
da k’irjin Gwaggo bada sautin damm!
damm!.. Amma cikin k’arfin hali, dake
shaid’an ya mata kururuwa, tace”sai me
in ka sakeni?.daman wani abu nake
samu a gidanka, in banda gayyan tsiya.
Malam ya d’aga hannu yace”Ya Allah
kana jina, kana ganin abunda ke faruwa,
Ya Allah ka azurta Khadi da abunda zata
taimaki Hauwa’u. Yana dasa aya,
Gwaggo tace” ba amin ba har abada, sai
dai ku da wannan mayyan, talashe
zuciyarku.
Fuuuu Gwaggo takama hannu Rabee,
tajuya ta kali Beebah, kee da ta lashe
maki zuciya, saikiyi ta makale mata,
suka shiga d’aki.
Malam ya kama hannu Khadi, da Beeba
ya kaisu d’akunsa, albarka ya samusu,
ya musu nasiha, tare da k’ara bama
Khadi hak’uri. Tace” Baba ba komai, ae
Gwaggo uwatace, ita na bud’i ido na
gani, ita na santa, kuma ina mata fatan
Allah yasa ta gane Ameen ya amsa.
Dr Umar kuwa, yana komawa gida, ya
tarar da Mum d’insa, suna hira da Ilham,
shima zama yayi, tare dacewa washh,
Mum tace” daga ina haka Son?. Gyara
zama yayi, ya kali Mum yace”daga
gidansu Khadeejat nake. Kafin Mum tayi
magana Ilham tace”bros nikam ina son
gani Aunty Khadejat d’inana. Kulum sai
labarinta mukeji, fuskansa cike da
murmushi, yace”zaki ganta har sai kin
gaji da ganinta ma. Mum tace”
Alhamdulilah! Allah ya nunan ranan da
Babana ya samu wacce yake so, sai fatan
Allah ya kaumu lokacin biki, cike da
zumu d’i ya amsa da Ameen. Dr Umar
yace” Mum baki ga yarinyan bane, gata
da hankali, kuma inkinji rayuwanta
abun tausayi, nan ya basu labarin
had’uwansu, da irin wahalan, su Mum
da ilham sun tausaya mata. Ilham tayi
karaf tace” bros to ina wacce katab’a
ban lbr ta, itama wacce Khaji a agun Dr
Abdul?. Ummm itakam har yanzu ba
labarinta. Mikewa zai haura sama,
yakali Mum yace”yau she Dad zai dawo
daga Dubai d’in?. Umma tace” umm sai
next week. Ok! Allah ya kaimu.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-61~65.
Sai da ta dad’e kafin, ta d’an tashi,
sannu suke mata, bata iya amsawa ba,
sai da ta huta sosai, Dr Umar ya kaleta,
cike da tausaya, Yace”yan’mata mai yake
damunki haka?. Da har kike irin
wannan tunanin?. Kasacewa komai tayi,
sai da yamata fad’a sosai, Yace” ki tashi
mukauki gida, sai a lokacin ta zaro ido,
kai ta girgiza musu alamar a’a, bayanda
basuyi ba, amma fir taki, daga k’arshe
Dr Umar ya tsara mata Napep, nan ta
bada kwatance gidansu, sai da tashiga
Napep sun d’au hanyan, Dr Umar ma
motarsa yashiga, har yayi hanyan gida,
komai tuna ya juya kan motarsa zuwa
Dakata, gudu yakeyi sosai, cikin sa’a ya
hango Napep d’insu, a baya ya rinka
binsu har suka kai k’ofar gida. Mai
Napep ya tafi, ta tsaya a k’ofar gida,
tana tunani shiga, gashi yamma tayi
sosai, ga yunwan da takeji, da kyar ta
iya shiga gidan. Ganin ta nufi cikin
gidan ya fito daga motarsa yazo dai-dai
zauren.
Assalamu’alaikum ta fad’a cike da tsoro,
kara shiga ciki tayi ganin Gwaggo bata
kusa, da sauri Gwaggo ta fito,”kee
karuwa yar’iska ina kika fito?. Cikin
fargaba da zaro ido, Khadi tace” wallahi
Gwaggo gun d’inki naje. “Karya kike dan
ubakiki, dukanta Gwaggo tayitayi kamar
ta samu jaka.
Dr Umar tun daga, nesa ke jin murtan ta
tana ihu, sai leke yaykeyi, zuciyarsa na
tafarfasa, ganin Gwaggo ta d’auko
muciya, Beeba da ke gefe sai kuka
takeyi, tana bama Gwaggo hak’uri, Dr
Umar dake cikin zaure, ganin Gwaggo,
ta d’aga muciya zata kwada mata, bai
san lokacin da ya shiga gidan ba, rike
muciyar. Gwaggo cikin fushi, d’ago tana
masa kalon raini, daga kai waye ne?.
K’ok’arin fincike muciyar takeyi, Malam
da ya dawo daga tafiya, yaji da sauri ya
k’araso cikin gidan, ganin abunda ke
faruwa yace”Hauwa mai kikeyi haka?.
Nan fa tafara ba Malam labarin karya da
gaskiya, ta d’aura dacewa”Khadi karuwa
ce yar’iska, da sauri Malam ya dafe
kansa, don harcikin zuciyan sa, yaji
kalman ta dake shi. Cikin kunan rai, Dr
Umar yace”wannan sharri ne wlh, nan
ya kwashe abunda ya faru ya fad’a
musu. Gwaggo nan ta tire, “sam ni
banyarda ba, shine ya d’auketa suke
iskanci tare, Malam ya mata kwalon uku
saura kwata, hak’uri ya fara ba Dr
Umar, tare da masa godia. Dr Umar yayi
musu salma ya nufi gida, cike da
jimamin rayuwan Khadi.
Tun daga wannan ranan, Dr Umar
yasamu gurin zuwa, gidan gun Malam
susha hira sosai, wani lokaci Malam ya
turo Khadi su gaisa, sam bainuna musu
ko shi waye ba, kuma bai taba sayan
wani abu ya basu ba. A hankali
shak’uwa ta shiga tsakaninta da Dr
Umar.
Kamar kulum Dr Umar, yayi wanka
cikin manyan kaya, yayi kyau sosai, sai
da ya biya ta, Sahad store yayi sayya,
kaya ya had’a ma Khadi, less da atamfa
da shadda d’inkaku, da su takalma da
jaka.
A hankali yake tafiya, har ya shigo
unguwan, cikin sa’a ya samu Malam na
gida, sai da suka gaisa, ya bud’e boot din
motarsa, buhun shinkafa biyu, na tuwo
dana dafawa, sai taliya carton biyar da
makaroni, harda su maggi star. Malam
dake gefe, ya tsaya yana kalon ikon
Allah. Sai da aka gama shigarwa,
Yace”Umar mai yasa kayi irin wannan
d’awainiyar, kai ya sunkuyar, Malam ae
ba komai, kai mahaifi ne ae. Godiya yayi
masa sosai, dai-dai lokacin, Khadi tafito
Gwaggo ta aike ta, tazo wuce musu, ta
gaida Dr Umar ya amsa cikin kulawa
zata wuce, Yace”tsaya ki amshi sak’onki,
don ina sauri yau, wasu manyan ledoji
ya miko mata, Malam Yace” Umar
d’awainiyan yayi yawa, bakomai Baba
sauri nake, sai na dawo, godiya yayi
masa Dr Umar yaja motarsa ya bar
gidan, Khadi ne tafara shiga cikin gidan
da laida, Malam na biye da ita. Gwaggo
tana ganin laida a hannu Khadi, da sauri
taso zata amsa, ganin Malam tace”yau
samuwa mukayi haka?. Malam yace”eh!
Wallahi wanda ya taimaka ma Khadi ne
yayi mana alkairi, Gwaggo ta dafe k’irji
lokacin ta zazzage kayan ciki, nan fa ta
tsorata, “ae wallahi abunda bazai
yuwuba kenan, wannan k’arya ne.
Malam daman funa furci ka kula shine
ka tsiri kai Khadi koyar d’inki, don kana
son ta had’u, da wanda ya kawo kayan,
mai yasa baka tura Beebah ko Raee’atu
ba?. Sai Khadi, nan tafara tonan silili ma
Khadi, cikin takaici Malam ke kalonta.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-76~80.
Da sauri ya tareta, ta fad’a hannusa,
sunanta yakira, Khadijat! Khadijat
Khadijat… Pls ki tashi, kar ki tafi ki
barni lokacin dana ke bukatarki, kene
farin cikina. Pls Khadijat, yana jijigata,
amma sam ko motsi batayi, Dr Umar ya
fita a hayyacinsa, sai sam batu yakeyi,
Gwaggo ko wani ruwan sanyi, tasake
d’ebowa bata tsaya, wata-wata ba, ta
k’wara ma Dr Umar. Duk da na da lafiya
sai da ya razana, ajiyar zuciya ya sauke,
nan take ya dawo cikin hayyacinsa,
hannu sa ya kala, da sauri ya d’auketa,
cikin mota ya sanya ta. Da gudu yabar
unguwan. Asibitin Murtala ya wuce,
yana zuwa ya d’auketa a hannu,
Emergency yayi da ita. Kasancewar shi
duty safe ke dashi, Dr Abdul ke duty
kwana. Da sauri ya d’aga waya ya
kirashi, “Dr Abdul dan Allah kazo
Emergency, Khadija tace bata da lafiya,
kazo ka taimka min, muryansa kaman
zaiyi kuka, duk ya rud’a Dr Abdul, don
bai kuma taba jin, Dr Umar cikin
wannan, yanayin ba. Dr Abdul
yace”Friend wacece Khadija?.cikin fushi
yace”Malam in zakazo to in bazaka zo
nakira, DR James, kashe wayan yayi,
yafara kiran Dr Jame kenan, Dr Abdul ya
turo qofar ya shigo. Da sauri yayi kanta,
yana ganin Khadi ce, mamaki ya cikasa,
tambayoyi yafara yi makansa,” daman
Umar yasan Khadi ne?.
“To mai yasa yarinka min tambayoyi
akanta?.
“Ta ya’akayi tazama Khadijansa?.
Maganan Dr Umar ne ya dawo da shi,
daga dogon tunanin daya shiga.
Dr Umar Yace”kai Malam, lafiya kake
mata, irin wan kalon?. Da sauri yazo ya
kareta, cikin kishi da jin haushi, yake
maganan. Dr Abdul bai cemasa uffan ba,
cikin hanzari yasoma dubata, daman
yariga yasan matsalanta, cikin ikon
Allah, ansamu numfashin ta, ya dawo
dai-dai. Sai dai bata farka ba, sun mata
aluran baci, don ta samu hutu.
Special room aka kaita, don hutawa ita
kad’aine a d’akin. Dr Umar ya zauna, a
bakin gadon ya zuba mata ido, ko
kyaftawa ba yayi. Ji yake kaman ya
k’arba mata ciwon, Dr Abdul ne ya
shigo, yace”Ya mai jiki?. Da sauki ya
bashi amsa. “Allah ya k’ara sauki. “In ka
gama kasameni a office d’ina. Ok! Dr
Abdul ya fita, office d’insa ya koma, ya
zauna cike da tambayoyi, a fuskansa. Dr
Umar sai daya kai, kusan kamar 1hrs,
kafin ya kira nurse, yace”ta kulamasa,
da patient d’insa.
Da sallama ya shiga office d’in Dr Abdul,
bayan ya zauna ne, Dr Abdul
Yace”friend ina kasamu Khadi?. Ko
dama ka santa tun-tuni, Dr Umar yace”
kai ka santa ne?. Dr Abdul ya d’aga masa
kai alamar eh!. Ajiyan zuciya Dr Umar
yayi, nan ya kwashe labari, tunga randa
ya fara ganinta, har yanzu, dayake fama
da azaban sonta. Sai da Dr Abdul ya
jijina kai, yace”Allah mai iko, to ae itace
Khadijan, da ranan kaji ana case akanta.
Cikin mamaki Dr Umar yace” mai kace
ne ban fahimta ba. Nan Dr Abdul
yabashi labarinta, iya yanda ya sani.
Umar ya tausaya mata ba kad’an ba,
wani Sonta da Qaunarta, suka k’ara
shigansa. Cikin tsokana Dr Abdul yace”
friend amma gaskiya, ka cika kishi,
kawai don ina mata kalon sani, amma
kawani tare, dariya Dr Umar yamasa,
tare da kai masa dukan wasa.
Malam dawowansa, daga kasuwa kenan,
aka basa labarin, abunda ya faru bai iya
shiga gidan ba, ya juya zai tafi kenan,
yaga Beeba ta fito, duk ta rud’e hijab ma
bai-bai tasa. Da sauri ta bisa, Napep ya
tsara musu, suka nufi Asibitin Murtala.
Zuciyan Malam sai tafasa yakeyi, yana
tunanin wani kalan hukunci, zai yanke
ma Gwaggo. Don abuntan yayi yawa,”to
wai mai Khadi ta tsare mata a
rayuwanta ne?. Da takeson ganin
bayanta, tabbas zai Aura da Khadi, don
ta huta da bala’in Gwaggo.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-71~75.
Khadi kulum tana cikin k’unci, Gwaggo
ta sata a gaba, baran in taga, Malam ya
fita kasuwa. Gashi Dr Umar ya kwana
biyu bai zoba, d’inki ma, tabar zuwa
sabida bala’in Gwaggo, wai sai Malam ya
saka su duka, don su Beeba su samu
suma mai saya musu kaya. Malam ko
yace”bata isa ba, tayi k’ad’an ta gindaya
mishi sharad’i yabi. Tunda tun farko,
Khadi ne tafara cewa tana so, dan haka
ba zaisasu ba. Zaban tayar musu da
hankali yasa Khadi ta samu Malam tace”
Baba bana jin dad’i zan d’an huta da
zuwa aiki, kafin wata sati, Tukun ya
hak’ura.
Dr Umar ko, bai da tunani da yawuce na
Khadijat, so ya kemata, wanda shi
kanshi, bazai iya auna shi, a mizani ba.
Masu karatu zamu so musan,
WAYE DR UMAR?
Umar Adam Naira, shine cikaken
sunansa, d’a, d’aya tilo girin Adam
Naira. Adam naira haifafen d’an Kano
ne, nan yayi karatunsa, har ya girma, ya
Auri maransa Maryama, sun dade da
aure, Allah bai basu haihuwa ba, sai
daga baya Allah ya azurta su da
haihuwan Umar, wanda yaci sunan
Baban Mum d’insa, bayan shekaru da
yawa, ta haifi Ilham, wacce itace auta, a
yamzu haka. Alhaji Adam Naira yarike
muk’amai, na gwamnati da dama.
Wanda yanzu haka shine gwamnan
Kano State mai ci. Ya kasance mutum ne
mai kwatanta gaskiya da adalci, hakan
yasa al’uman garin Kano ta Dabo suke
sonsa. Tunda Umar ya taso, shi bamai
son yawan, hayaniya bane, sannan bai
kula yan’mata,sai wata yarinya, Sakina
da ta makalemasa, sam bata cikin
tsarinsa, don bata da kamun kai,
yar’gidan, matai makin governor ne,
gata da rashin kunya, shiyasa basa shiri.
Yanzuma saukin da yasamu, ya dawo
yasamu sun fita waje, ita da Mum d’inta.
Iyayensa burinsu shine, yayi aure amma
baya kula yan’mata. Tun randa ya had’u
da Khadi, tunda yasanar da Mum d’insa,
da murna ta, tasanar da His Excellency.
Yayi farinciki ba kad’an ba. Yace” yana
dawowa zasu samu iyayen yarinyan, ayi
magana a sanya rana.wanna shine
labarin Umar a takaice.
Dr Umar zaune yau, sai tunanin
Khadijat, da ya damesa.
Key mutarsa ya d’auka, yana fitowa
securitys, suka fara gaidasa, da gudu
suka bud’e masa, k’ofar motan yashiga,
gida ya nufa yayi wanka, dun zuwa gun
Khadi. Yayi kyau sosai, ya shiga mota shi
kad’ai batare da security’s ba, ya nufi
gidan.
Khadi ko tunda ta tashi, tashi tana son
yin wanka, kayan da Dr Umar ya kawo
mata. ta d’auko wani less, mai kyau
purple da duwatsu farare a jiki. Tayi
kwaliya sosai, ta kuma yi kyau.
Kasancewan yanayi gari, da sanyi, gun
sai yayi, bada yanayi mai kayatarwa.
Gwaggo ta shiga makwabta, sai zuba
take musu. Yaro ne yashigo”wai ana
salama, da Khadijat inji Umar.
Tace”kace ina zuwa. Yana fita ta d’auko
hijab d’inta fari tasa, bakaramin kyau
tayi ba. Cikin nutsuwa ta fito, tunda
Umar ya hangota, zuciyar sa sai
harbawa, ido ya k’ura mata.
Gwaggo da tafito daga, gidan su abula,
ganin Umar acikin k’atuwar mota, nan
zuciyarta ya fara tafarfasa. Yau mai
zanyi ma Khadi na huce?. Wata zuciya
tace”kawai ki d’auko wuka ki burma
mata. Mtss a’a za’a kamani, can shaidan
ya tuna mata, kawai ki shek’a mata
ruwan sanyi, tunda bata so. Da sauri ta
koma gidan Abula, tace”dan Allah samin
ruwan a fridge d’inki. Sam Abula bata
kawo komai ba, ta iba mata, a karami
roban plastic. Da sauri tayi gida, ta k’ara
dana randa, kamar wata mahauk’aciya
ta fito.
Dr Umar ya shagala, da kalon Khadi,
itako tana wasa, da yan’yatsun hannuta.
Sai jin shaaa… sukayi, take idon Khadi
ya kafe, numfashinta ya d’auke, ta tafi
luuuuu zata fad’i kasa. Da sauri Dr Umar
ya fito, yana kiran sunanta, tareta yayi
ta fad’i a hannusa yana jijigata, amma
sam bata ko motsi.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺗﻠﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-81~85.
Malam sun isa Asibiti, direct office d’in
Dr Abdul sukaje, Don tambayansa, ko
nan aka kawo Khadija, don shi har
yanzu, bai san a ina, Dr Umar yake aiki
ba. Duk da yasan dai, shi likita ne, suna
zuwa suka tarar da Dr Abdul a office,
cikin yanayi damuwa Malam”ya
gaidashi, ya tambayes ya aiki?.
Alhamdulilah!, Malam yace”Dr dan
Allah, ko nan asibitin, aka kawo Khadi?.
Dr Abdul ya amsa masa da eh!. Barin
rakaku d’akin da take. Sai da sukayi
tafiya mai d’an nisa kad’an, kafin suka
shiga, wani Ward mai kyau, kana shiga,
falo zakagani babba, sai gurin da likitoci
ke zama, gefe kum d’akin hutun likitoci
ne. Sai d’akuna da suke jere, gwanin
birgewa, gurin tsab da shi, kamar ba’a
cikin asibiti ba. Kowani d’aki gado
d’ayane a ciki, sai yar loka da ke gefe,
Malam suka tura, qofar d’akin da
sallamansu. Dr Umar ne zaune ya zabga
tagumin gaban Khadi, sam bai masan
sun shigoba, suka sake mai-maita
sallama, amma shiru, Dr Abdul ne ya isa
gunsa da sauri ya dafasa, yace”my
friend, cikin razana ya d’ago, sai a
lokacin yaga Malam, duk kunya ta
rufesa.
Mik’ewa yayi da sauri, yana musu,
sannu da zuwa. Kalo d’aya Malam yayi
ma Khadi, yaji wani mugun tausayinta,
ya kamasa, tambayan kamsa yayi anya
bayi da laifi, shima acikin cutar da
Khadi, da Gwaggo takeyi?. Idonsa ne ya
ciko da kwala, bakin gadon yaje, ya rike
hannuta, cikin muryan damuwa,
Yace”Khadijatu kiyafr min, duk nine
silan saki, cikin wannan damuwar.
Tabbas Hauwa watarana sai tayi
nadama, mai d’umbin yawa, Allah ya
miki Albarka, ya Allah kajikan Adamu.
Duk wanda suke gurin saida jikinsu yayi
sanyi, Beeba kam kuka takeyi sosai.
Malam ya juya ya kali, Dr Umar
yace”Umaru na rasa, da wani irin,
kalma zan gode maka. Tabbas ka taimaki
Khadijatu iya taimako, Allah ya bamu,
abunda zamu saka maka dashi.Allah ya
maku Albarka
Cikin zuciyan Dr Umar yace”abida
zaumin kad’ai kubani Khadijat, don
zuciyata, takamu da azaban sonta.
Gwaggo da ke gida, sai fatan take, “Allah
yasa adawo, da gawan Khadi. Na tsani
ganinta, kamar mayya, komai zakamata
bata zuciya. Mtsss ina da daga nan,
tashiga uwa duniya, in huta da
fitinaniyan, yarinyannan.
Ko da taji Beebah tabi Malam, sun tafi
asibiti, bakaramin haushi tajiba.
Tunanin kalan, rashin mutuncin da zan
masu.
Kwanan su Khadi, biyu a Asibiti, Dr
Umar shi ke d’awainiya da su. Kulum
yana hanyan Asibiti, yana tashi daga
aiki bayan ya duba Khadi, shagon waya
ya zarce, yasaya mata, iPhone 7, wayar
ta had’u. Gida yanufa, yana zuwa, yayi
wanka, ya fito dining, Iham ce tazo
tazauna a gefensa, tana masa surutu, can
idonta ya kyalo waya maroon, tace”bros
wannan fa?. Tare da kai hannuta ta
d’auka, “bros wayan tayi kyau, bai
kaleta ba Yace”na Khadiyat ne, ihu tasa
tare da cewa”wooow wayan tayi kyau.
Barin samata number, nan harda
WhatsApp, ta bud’e mata. Sai da yagama
tukun ya amshi wayan yafita.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-86~90.
Sai da yayi musu, sayya mai yawa, ya
nufi Asibiti. Ko da ya shiga, sai da ya
biya office dinsa, ya ajiye wasu files,
kafin ya nufi ,d’akin da su, Khadi suke.
Da sallama ya shiga, suka amsa masa.
Beebah ne “ta gaida shi, cikin
girmamawa ya amsa, “ya tambayeta ya
mai jiki?. “Ba shi amsa da sauki
Alhamdulilah!. Fita tayi ta basu guri, ya
kali Khadi da ke kwance, “ta gaida shi,
cikin muryan, marasa lafiya, “ya amsa
mata, tare da tambayan ya jikinta?. ta
bashi amsa da sauki. Ido ya zuba mata,
har saida tasoma jin kunya, ajiyar
zuciya ya sauke, ya kara lumshe idonsa,
a hankali ya bud’esu, cikin wani salo, da
karya murya, ya kira sunan Khadeejat!!!.
Duk da rashin lafiyan da take fama
dashi, sai da taji, jikinta yamata, wani
iri,”Na’am ta amsa masa cikin siririyan
muryanta. Ya kaleta, yace”Khadeejat!.
Na kasa hak’uri akanki, Khadeejat!. Ki
taimaki zuciyata, da take fama da
azaban sonki, My Khady tun randa, na
fara d’aura idona a kanki, nakamu da
qaunar ki, ki taimaka in samu gurbi, a
cikin zuciyarki. Duk maganan, da yakeyi
Khadi, bata ce komai ba. Sai lumshe
idonta datayi, kamar mai jin bacci, cikin
kasa-kasa da murya, harda d’an
sauk’owa daga kujera, Yace”pls
Khadeejat ki taimaki rayuwata. Tabbas
nasan ina aure ki, a matsayin mata,
kuma uwar ‘YA’YA NA, nasan zasuyi
alfahari dake, a matsayi uwa ta gari.
Khadeejat!. Ki sani duk wani abunda
akeso, mace ta gari ta had’a, kin had’a.
Khadeey na!! I’m deeply in ur love,pla
don’t let me go!! You d joy of my lyf, pls
n pls Khadeey!!, ki samamin matsuguni,
a zuciyarki, ko k’ad’an ne.
Ganin shiru batace komai ba,
Yace”Khadeetaul~Kubrah, in kin amince
pls ko murmushi, kimin in samu sanyi, a
zuciyata. Ganin shiru yasa yanayinsa ya
canza, duk da idonta na rufe, tana iya
ganinsa, amma shi bai lura, da hakan ba.
“Wani lallausan murmushi ta saki, tare
da rufe fuskanta. Ganin haka, ya sauke
ajiyar zuciya, yayi godiya ma Allah. Juya
masa baya tayi, duk yanzu kunyansa, ta
soma ji, ya dad’e yana mata hira, ganin
tana jin kunyarsa, ya ajiye mata waya
tare da mikewa, Yace”yau k’anwata
kunya na takeji, amma badamuwa,
wataran zanyi maganin kunyan nan.
“Ga wannan d’an ajima zamuyi waya,
ya fita abunsa, a waje yayi sallama da
Beebah. Ko da tashi go d’aki, lokacin
Khadi ta mike, sai murmushi take
zubawa, Beebah tace”Addah lafiya
naganki cikin wannan fara’a?, cikin
zumud’i ta labarta ma Beebah, itama
tayi murna sosai,nan suka bud’e, kayan
da yakawo musu, yasha addu’a kam,
suna bud’e na waya, kalo ya koma
kansa, sun yaba da kyan, wayan sosai.
Sai can dare taji wayar na k’ara, ko da
tad’aga wayar kasa d’aukan kiran, duk
sun rasa ma ya’akeyi, Beebata tayi nata
basiran ama ina! Har wayan ta yanke,
sai can dai Khadi tace”tsaya inaga
wannan, ruwan ganyen ne amsa kira, do
d’azu jan ya katse ne. Tana jan ruwan
ganyen, ta tafara jin magana.
Assalamu’alaikum! Wa’alaikumusalamu!
Ta amsa, sai tayi shiru, ”
Khadeejat ya jikin?. “Da sauki
Alhamdulilah!. Hira ya rinka janta dashi,
har sai da yaji, kamar bacci na son
d’aukanta, ya kyaleta.
Kwanan Khadi 7 aka sallameta, tayi fress
kamar batayi rashin lafiya ba, suna
dawo gida, suka samu Gwaggo bata nan,
suka shiga, harda Dr Umar ganin irin
yanayi, d’akin da Khadi take kwana,
ransa ba dad’i ya kira waya, ba’a fi
minti talatin ba, sai ga mota da sabuwar
Katifa, irin manyan nan, da filo da
bargo, aka gyara d’akin fess, ya musu
sallama ya tafi, ko da Malam ya dawo
yayi godiya, ana haka sai ga Gwaggo.
Yau kam ta cika kamar zatayi hakuka,
don ba haka taso ba, taso a fitar da
kayan amma Malam ya hana. Rayuwa
sai tafiya yakeyi, soyayya tsakanin Khadi
da Dr Umar sai abunda ya karu, kulum
suna gaisawa da Ilham, harta sata a
group d’in novel ta yi kawaye yanzu.
Duk inda kake da jama’a, baka rasa yan
gulma, acikin mukaraban, Dr Umar
ansamu wanda ya sanar da Sakeenat, Dr
Umar yana neman wata yarinya, yanzu
haka ana kan shirin magana Aure, nan
take hankalinta ya tashi, bashi ta biyo
jirgi yau ta tazo 9ja.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-91~95.
Karfe shidan yamma, jirgin su ya sauka,
acikun garin Abuja. Bata bata lokaci ba,
ta sake shiga jirgin Kano, ko da ta iso,
anyi sallah magriba, ana shirin yin
isha’i, taso yau taje taga yar gidan uban
waye, Dr Umar ke sonta, kuma da me
tafita da shi, da har zai aureta, tabbas
yarinyan sai ta raina kanta, washe gari
da had’a security dinta, wankan kece
raini tayi, ta kira kawarta, Zulaihat
tace”Zuly ki shirya kizo, zaki rakani,
wani karamin unguwa, wai shi Dakata.
Cike da tsokana Zuly tace”kawas mai
zaki dakata acan, nan Sakeenat, ta sanar
mata da komai, Zuly tace”ban minti
kad’an ina zuwa ko ku biyo ku d’auken.
Haka akayi, suka dauketa, cike da rashin
mutunci a fuskokinsu.
Khadi ko wanka tayi, sabi da tasan yau
weekend, Ya Umar d’inta zaizo, tayi
kyau kamar wata amarya. Suna tsakar
gida suna tad’i’ ita da Beebah
kasancewan, Gwaggo ta tafi gidan
kawarta, shiyasa suka sami freedom yau.
Tun daga nesa suke jin, wi wi wi wi,
kukan jiniya alamar, wani babab yazo
unguwan, har sai da aka zo qofar
gidansu, tukun kukan ya tsaya, cikin
mamaki suna jira suji maisu shigowa,
Khadi tace”Beeba kardai police ne suka
zo gidannan?. To wayayi laifi?. Tana
wannan tunani ko taga masu bakaken
kaya, suna shigowa cikin gidan, nan take
hanjin cikinta ya kad’a.
Sai da suka shigo, sun tsatsaya musu,
wasu yan mata ne biyu, su ka danno kai
cikin gidan, kalo d’aya zaka musu ka
gane, sun san bariki, idonsu abud’e
yake, ga fiskansu ta sha man bleaching.
Cikin isa da taunar chewing gum, ta iso
gaban su, sai da suka musu kalon, sama
da kasa, kafi ta juya, ta kare ma gidan
kalo. A tare suka kwashe da dariya, Zuly
tace”kai yayan talakawa, a cikin ku
waye Khadi ko Khadija, shiru ba wanda
ya bada amsa. Cikin zafin rai suka sake
magana, da kyar, Khadi tace” gani nice
Khadi. Sai da suka kaleta sama da kasa,
sai da gaban Sakeenat ya bmfad’i don
sai yanzu ta lura da Khadi, tabbas
yarinyan ta had’u, dole Dr Umar ya
makance a sonta. Daurewa tayi, ta fara
yi ma Khadi, “concrete warning, duk
randa naji ance kin kula Umar sai na
muki rashin mutunci, sai nasa an
d’aureki, tabbas duk halin naka-naka ne,
mai rashin kunya ma wataran yana da
rana. Beebah da Khadi kasa magana
sukayi, Rabee’at dake bacci a d’aki,
hayanayi ya fitar da ita, jin yanda, aketa
zaginsu, dana iyayensu ta karaso da
gudu, ta kalisu Sakeenat, ta sama da
kasa, ta nuna su da yatsa, tace”banza
mai fiskan biri, kin wani sha bleaching,
waye ke?. Da har zakina zagin iyayena,
nan Rabee’at tashiga sauke musu,
kwandon rashin kunya.
Dr Umar yayi wankan sa ya nufo, gidan
su Khadi, tun da ya shigo unguwan ya
fara ganin motoci, har ya iso qofar
gidansu Khadi, nan yaga security, gidan
gwamnati, da sauri ya fito daga mota, ya
kira wani body guard, tambayesa mai ya
faru, nan yake basa bayani, Sakeenat ne
a ciki, da sauri ya shiga gidan, dai-dai
likacin da, Sakeena ta harzuk’o zata
mari Rabee’at da sauri Khadi, ta shiga
tsakanin su, sai jikayi tasss!!, karan
saukan mari a fiskan Khadi, kafin ta
motsa, sai nasojin wasu karan tass!!
Tasss!! Tass!! Gar sau uku, Dr Umar ya
mari Sakeenat. Ya juya ya kali security
d’in, da sauri suka bar cikin gidan. Cikin
fushi ya kali Sakeenat, Yace” kee waya
baki izinin zuwa gidan nan?. Duk randa
na k’ara, ganin k’afarki sai kinji
ajikinki, ki kuma sani Khadeejat ta miki
nisa, itace uwar ‘YA’YA Na, ita nakeso,
itace rayuwa, farinciki na, in part
rayuwata bazatayi dai-dai ba in ita,
banza sakarya, ko ana soyayyan dole
ne?. Nace bana sonki bana sonki, ba
kuma zan soki ba. Cikin b’acin rai yazo,
rik’o hannu Khadi yace”My wife kiyi
hak’uri dan Allah, hannu yasa, ya share
mata hawayenta. Ya rike hannuta, ya
Sakeenat da bakin ciki ya isheta, kaman
ta shid’e a gurin. Yace”kee Sakeenat!
Kinga wannan ta fi minke komai, itace
mahad’an rayuwa ta, tafiki kamun kai,
da nutsuwa, in kin…… Da gudu ta bar
cikin gidan tana kuka, wi-wi da hawaye.
Tabbas yau taja ma kanta raini agaban,
wayanda take takasu son ranta, yau
Umar ya mata haka?. Tana fita mota
tashiga, Zuly ma ta biyota, rake suka bar
unguwan.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-96~100.
Tana fita suka nufi gida, da gudu ta
shige d’akinta, kuka ta rinka rusa sosai,
Hajiyarta ne ta shigo, tace”Zuly mai ya
sami k’awarki ne?. Zuly tafara bama
labarin komai. Hajiya tanisa
tace”Zulaihat ba ki ba ma kawarki,
shawara mai kyau, tunda Umar baya
sonta, sai ta hak’ura, ko ana son dolene,
kusani a ko da yaushe mace, ita ke jan
kimarta, nikam bazan goyi bayan k’arya
ba. Kunutsu kusan mekukeyi kun fa
girma fa, ae ko irin shigan da kukeyi,
wazai so ku?. Inayi fad’a Abban su
Sakeenah, yace nacika takura masu, ga
irinta nan, nima ina goyon bayan Umar,
matsawan ba canzawa kukayi ba. Kukan
Sakeenat ya karu, sai buga k’afa takeyi,
tana cewa”Hajiya ni baki sona, tunda
bakison abunda nake so, “tsawa ta daka
mata, ke bana son aakarcin banza da
wofi fa, sai da tamusu ba dad’i, tukun ta
bar d’akin.
Dr Umar kuwa lallashin Khadi yayitayi,
Gwaggo ne ta shigo da sallamarta, tun
daga waje an fata rahoto, shiyasa take
fara’a, tana ganin Umar, tace” eehehe
duniya yau taimin dad’i, in dai a kanka
ne, da Khadi naso da dukan tsiya suka
mata, ka wani shigo mana gida d’an
iska, wato karuwanka ne suka kasa
hak’uri suka biyo ka nan?. Ran Umar in
yayi dubu ya baci, don ba abuda yatsana
kaman a danganta shi da mazinaci.
Gwaggo ta zagesu tass shida Khadi, tayi
d’aki, Beebah ko sai basu hak’uri takeyi,
Khadi kam kuka takeyi, kafansa yaja jiki
ba kwari ya bar gidan.
Malam ya na dawowa ya samu labari,
yajima yana tunani daga k’arshe, yace
anya kuwa bazan dakatar, da Umar da
zuwa gidan nan ba?. Haka ya ta sake-
sake, har ya tsayar da amsa ma kansa.
Bayan kwana biyu Umar yazo, tun a
waje suka gaisa da Malam, nan ya fara
ba ma Malam hak’uri, Malam yace”ba
komai ya wuce, amma inaga ka hak’ura
da zuwa kawai, tunda daman ba wata
alaka bace a tsakanin ka da Khadeejat,
cikin firgici ya d’ago, yanaso yayi
magana ya kasa, Malam yajima yana
zargin Umar na son Khadi, amma bai
furta ba, shiyasa yayi hakan don ya
tabbatar. Don zan bada dama ga mai
sonta ya turo magabatan sa, ayi magar
Aurenta kawai. Inaga hakan shine zai
zame mata hutu, Umar duk ya rud’e,
yakasa magana jiki ba kwari, yabar
unguwan, gudu yakeyi Allah ne ya kaisa
gida lafiya, yana zuwa ya tarar da Mum
a falo, gunta ya nufa, ya kwantar da
kansa, a kan cinyanta, sai ga hawaye.
Cikin sanyin murya yace”Mum zan
rasata, Mum ki taimaka min, pls dan
Allah!. Cikin rashin fahimta Mum
tace”wacece zaka rasata?. Ajiyar zuciya
ya sauke, Yace”Mun Khadeejat ce, Mum
tace”kamar yaya zaka rasata?. Nan ya
kwashe labari, ya fad’a ma Mum komai.
Tab lallae Sakeenat bata kyauta ba,
amma ko da Dad d’inaka bai dawo ba
zamuyi waya dole asan abinyi.
A yan kwanakin nan duk Dr Umar ya
rame, hakan yasa Mum, ta sanar da Dad
d’insu, ko da sukayi magana dashi,
yace”bazai samu daman dawuwa, a
satin ba don haka zai sa mataimakinsa,
yaje da kansa, Mum tace” ni a’a ban
yarda ba, kasan Alhaji Bashir baya da
sauki, akan yara , kawai inaga zamu
nimi wani yaje, kuma kaga yanda
yakeson Sakeenat, komai zai iya yi. Dad
yace”shikenan duk yanda kukayi, Mum
ta sanar da Umar komai yayi murna,
sanna yace”shi yanaga a tura Baba
Liman, don yana da halin dattaku. Haka
ko akayi, Baba Liman yaje neman auren
Khadi ma Umar, basu wani samu
Matsala Baban Khadi ba ya amince. Nan
suka zuba kayan mun gani anaso, da
kud’in gaisuwa dubu 2k, Malam yaki
karba yace sunyi yawa, amma Baba
Liman ya dage sai da ya karba. Da
murna yashiga gida, a zuciyar shi, yana
mai cewa tabbas Khadijansa zata huta,
don da alama Umar d’an manyan
mutanene, kuma zai riketa da AMANA.
da murna ya shiga gun Gwaggo, cikin
zak’uwa takaleshi “Malam lafiya naga
sai farin ciki kakeyi?. Hmm kedai bari
kawai, ina cikin farin ciki, mik’omata su
gidan goro da catoons d’in minti yayi,
tare da d’aura mata damin kud’i akai,
ido ta zaro su waje, “Malam wayan nan
kud’in fa da kayan fa?. Cikin murmushi
yace”na Khadijat ne, kud’in aurenta.
Jakar uba! Ina bazai yuba, ina na Beeba
ko Rabee’atu?. To ba a gidan nan za’ayi
wannan abun ba, sai dai ko inda Beeba
ne. Malam yayi dariya yace”Hauwa
kenan wai meysa ba kya boye
hassadanki a fili, ae ni na d’auka Khadi
da Beeba da, Rabee’at, duk d’aya suke a
gunki?. Allah ya sauwake, nawa-nawa
ne. Kuma wannan auren bazai yuwuba,
sai dai ko in zaka kawo na Beeba sai a
had’a. Shikam dariya ta basa, don suk
tagama fita a hayyacinta, ya d’ibi kayan
ya kai d’akinsa. Khadi najinsu amma
duk ta damu da taji wa Malam zai
had’ata aure da shi?.
Malam ne ya shigo d’akinta, ya zauna a
kujera, cikin nutsuwa ya kira sunanta, ta
amsa, sai da yamata nasiha, kamar
yanda ya saba, tukun ya saida mata,
Umar ya kawo kayan ,yagani yana so,
ina fatan kin amince kina sosa?. Shiru
tayi, daga yanayinta ya gane ta amince,
albarka ya samata ya fita.
Washe gari Dr Umar yayi wanka sa, yayi
kyau sosai, sai da yabiya Sahad ya mata
shooping mai yawa, tukun ya nufo
gidan, yaro yasamu ya aika ta fito. Cikin
nutsuwa take takawa, tana sanye da
hijab ash yamata kyau, hannu tasa a
aljihu yana kare mata kalo. Da sallama
ta karaso bayan sun gaisa, yace”gimbiya
Khadeejatu, murmushi tayi yace kali
nan, tana d’ago fuska ya kashe mata ido
d’aya, tare da d’aga mata gira, duk sai
taji kunya ya kamata. Haka sukayi
hiransu a zaure, sai dab zai tafi ya d’ebo
mata, kayan saya mata, godia ta masa
har zata tafi yace”tsaya barin yi
surprising d’inki, murmushi tayi. Yace”
pls close ur eye, ba musu ta rufe, ” miko
hannuki, bata komai ba ta mika masa
tana murmushi, wani zobe ya ciro sai
kyali yakeyi, ya sanya mata a hannu,
nan take hannuta ya d’au kyalu yana
haskawa. Kiss ya kaimta a hannu, sai
sukaji, la ha ila ha illalahu, uhu jama’a
da sauri Gwaggo ta damke su duka. Ta
kwalala jama’a ku kawon d’auki na
kama yan iska yau. Ihu take kamar
mahaukaciya, Khadi ko duk jikinta sai
bari yakeyi, nan take hawaye ya fara
zuba, Umar ko don takaici kasa motsi
yayi.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
’YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-101~105.
Cikin takaici ya fincike rigansa, kalon
tsana yake mata, da sauri Gwaggo ta sha
gabansa, yau fa sai na tona muku asiri.
Wani mugun kalon da ya aika mata,
yasa Gwaggo bashi hanya, Khadi da gudu
tabar gun. Gwaggo ta ga kayan da Dr
Umar ya kawo da rawar jiki ta d’iba tayi
cikin gida.
Beeba na ganin haka tace”Gwaggo mai
yasa keke ma Addah Khadi haka?.
Gwaggo cikin zumud’i tace”kee bari
kawai ae ido da ido na kamasu suna
iskanci, cil da cil ganin annabin
tsohuwa. Beeba tace”kai Gwaggo gaskiya
Adda Khadi bazatayi haka ba, zata taba
zubar da mutuncinta ba, kuma na yarda
da tarbiyan da Malam ya bamu. Cikin
b’acin rai Gwaggo tace”oh to! to! Wato
Malam shi ya kula da tarbiyan ku bani
ba?. Beeba shiru tayi ganin Gwaggo ta
d’au da zafi.
Malam na dawowa Gwaggo da
munafurci tazo ta fara labartawa
Malam, Malam ya kaleta sama da kasa
yace”tashi ki ban guri bana son gulma, a
yanzu a kwai wani abunda zaki fad’an
na yarda, bacin nasan irin tsanar da
kikayi ma Khadija, yarinyan mai
hankali, bataji ba bata gani ba, kna
gallaza mata, jiki ba kwari Gwaggo ta
bar d’akin.
Dr Umar ko hankalisa kwance ke
gudanar da aiki, yanzu Dad d’insa kad’ai
ake jira a kawo sadaki, sai asaka ranar
biki.
Sakeenat kuwa sam Mum d’inta, taki
goya mata baya. Hankalinta duk ya
tashi, can ta tuno wata shawara, Zuly ta
k’ira a waya. Tace” kqwara kina ina ne
yanzu?. Zuly tace”gani a hanyan zuwa
gidan ku. “Ok sai kin iso. Ta ajiye wayar
tana zaman jiran zuwan Zuly.
Ko da Zuly tazo bayan ta gaisa da
Hajiyar Sakeenat, tashiga gun Sakeenat,
bayan sun zauna Sakeena tace”kawa
nifa bazan share mari da Umar ya
minba gaskiya. Zuly tace”wani mataki
zaki d’auka?. Sakeenat tace”na bayar a
sayo min dorina hud’u masu kyau,
zamuje unguwansu ba tare da securitys
ba, in munga yarinyan ko mu aika tazo
sai mu cazata.Zuly tace”good idea, haka
zamuyi.
Key motarta ta d’auka suka fita,nan idi
security ya kawo mata sak’onta, ta karba
suka ja mota sai Dakata.
Sun dad’e a unguwan Khadi bata fito ba,
can da suka gaji yaro suka tura yaro ya
kirata, Khadi ko kamar bazata fito ba,
amma can da yaron yasake dawowa, ta
d’au hijab d’inta tace”Beeba ana kira na
a waje barin duba ga wayata nan. Khadi
na fitowa yaron yace”gasu can a wancan
motar. Khadi tana ta raba ido, don Umar
bai tab’a zuwa mata da irin motar ba.
Sakeenat ko suka rike bulala kowa ne
bibiyi a hannusu, sai da Khadi tazo kusa
suka bud’e motar atare, suka nufota da
gudu dukanta suke tak’o’ina. Khadi ihu
take amma basu kyaleta ba, Beeba taji
kamar muryan Khadi da gudu ta lek’o
ganin ana dukanta, koma gida “Gwaggo
dan Allah kizo, yaran ranan suna dukan
Adda Khadi, Gwaggo tace”ha da gaske
Beeba tace”eh!.
Duka suka fito da gudu. Dukanta ko suke
Gwaggo ta fara kukara mata, kunyi min
dai-dai. Rab Beeba ya b’aci sosai, ganin
ba mai ceton Khadi, gashi ba maza a
gun, yasa ta tuna da Dr Umar. Da sauri
ta duba call history, ta kira number,
bugu biyi yad’aga, “hello hello Ya Umar
kazo ga wasu na ta dukan Adda Khadi,
wanda suka zo ranana. Cikin figici
yace”what suwaye?. Kashe yawar yayi
ya shiga mota gudu yake kamar zai tashi
sama.
Sakeenat ko ganin sun mata lilis, ga
mutane sun soma taruwa da gudu suka
shiga mota, suka bar unguwan.
Dai-dai zasufita a layi motar Dr Umar
yadanno kai ganin motar Sakeenat yasa
yasha gabanta, ganin zai tsaresu yasa
taja motar da k’arfi sai da ta buge masa
glass d’in mota ta gudu. Da har zai bita
sai ya tuna kowani hali Khadi take
kuma?. Sai ya fasa ya kara gudu.
Beeba ko ganin sun tafi dakyar wata
makwabciyar su, ta taimaka mata suka
shiga da Khadi gida. Karkuga fiskan
Gwaggo fal farin ciki.
Dr Umar na zuwa yaga mutane, da gudu
yayi salama ya shiga gidan, Beeba ya
fara karo da ita cikin damuwa ke
tambayrta ina Khadija?. Hawaye ya
k’ara zubowa “tana d’aki a kwance.
Yana shiga yaga halin da take ransa ya
b’aci sosai. Ya kira beeba yace” ki had’a
ruwan zafi don tayi wanka, waya ya
kira ba afi minti goma ba sai ga wasu
ma’aikatan asibiti da kaya, da kanta
yamata treatment, ya mata allura nan
take bacci ya d’auketa. Yana fitowa
yace”sistet Beebah barinje gida na dawo.
Na mata allura ta samu bacci, in ta tashi
ki kaimata ruwa ta watsa zataji dadi.
Yana zuwa gida yasanar da Mum d’insa
komai, cikin bacin rai takira His
Excellency yana d’auka, tace” ranka
shidad’e! Ya aiki?. Cikin jin dad’i His
Excellency ya amsa. Nan ta sanar masa
da komai, sai da ya jin-jina al’amarin
yace”tun da Baba liman nanan zan sa a
tura 1million sai akai sadaki, 2millions
kuma a had’a kaya akai. Ina dawowa sai
aure kawai. Mumcikin farin ciki
tace”Allah ya ja kwanan mai girma
governor, godiya muke Allah ya tsare
mana kai, Ya amsa da ameen.
Malam ko da ya dawo ransa ya baci,
amma yace”duk hakan baza’a fasa
auren nan ba sai anyi, duk mai hassada
sai dai yayi ya gama. Dr Umar ko kulum
sai yayi sawu 3 a gidan kula ta
musamman ke ba Khadi.
Yau da yazo bayan sun gaisa da malam
ya saida masa “iyayensa zasu zo, za’a
kawo sadaki. Malam yace”Alhamdulilah!
Allah ya kawosu lafiya mungode.
Washe gari Baba liman yazo ya kawo
sadaki, Malam sai da ya razana, kin
karban kud’in yayi yace”gaskiya Malam
sunyi yawa a rage. Baba liman yace”sam
bazan koma da ko si-si ba, mudai fatan
mu Allah ya sanya alkairi. Baban Khadi
ganin Malam ya girmesa, kuma bazai
iya masa musu ba ya sa hannu ya
karb’a.
Yana shiga gida don ya ba ma Gwaggo
haushi yace”Hauwa kawo min taburma
nan kizo kiga ikon Allah. Da sauri
Gwaggo ta fito har tana tun-tub’e, ta
shin fid’a masa tabarma bayan ya zauna
sai taga ya zaro da min kud’i har bunch
biyar, ido Gwaggo ta zaro, “Malam ina
kasamu wanna kud’i?. Murmushi yayi
yace”Hauwa wato zakaran da Allah
yanufa da cara ko ana muzuru ana
shaho sai yayi. “Kuma d’an hakin da
karaina wataran sai ya baka mamaki.
Gwaggo tace”ni dik ban gane hausanka
ba Malam?.
Malam yace”hmm Sadakin Khadi aka
kawo har naira na gugan naira million
d’aya. Wayyo nashiga uku sadaki ina
Malam d’an yankan kai ne ba fa
zaiyuba. Nima sai ka samo ma Bedba
miji, Gwaggo ta sha kwalan Malam, ihu
take tana kuka, tana fad’in ya cuceta.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
’YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-106~110.
Gwaggo ta sha kwalan malam sai ihu
takeyi, ya sa hannu ya ban-bare rigansa,
yazo zai wuce ta sake shan gabansa,
“yaufa bazaka fita agidan nan ba, yau
saika kawo ma Beeba miji. Ya matsa
tabisa yazo zai shiga d’aki ta tare qofar,
sai ya tureta yazo fita ya iso zaure, tazo
da gudu ta kama rigansa saida ta yaga.
Ran Malam in yayi dubu ya b’aci bai san
lokacin da ya kikifa mata mari ba, ya
hankad’ata ta fad’i akasa. Yace”Hauwa
hassadakin bazaikai ki ko ina ba,
wannan aure matsawan in ima raye ba
fashi, sai dai ki mutu da bakin ciki. Ya
juya ya nufi d’aki ya canza kaya, yazo
ya wuceta, har ya fita ya dawo
yace”kuma wallahi in kika kuskura kika
tab’a Khadija, a bakin aurenki saki zan
miki ba dawowa, kina dukanta kin san
sauran, Yasa kai ya fita. Gwaggo abun
duniya ya isheta, tabbas Malam tun da
ya rantse sai ya aikata, jiki ba kwari ta
koma d’aki tafara kuka, cikin zuciyarta
ko cewa take”wanna mari ba zai sha
banza ba tunda yace karna daketa, to ae
dole tayi aikin gida, dan haka ba duka
akwai zagi da wahala yankuma.
Khadi tana d’aki kwace, tana group chatt
da kwayenta, wanda suka had’u a
WhatsApp ta lura suna da hankali,
shiyasa nasu yazi d’aya. A group d’in
Khaleesat Haiydar suka had’u na
Facebook dake Khadi mayar karatun
novel ne. Hiran Novel d’in KAINE SIRRI
NA littafin Aisha Muh’od, Queen Neenah
tace” Khadeejat kin karanta KAINE SIRRI
NA? khadi tace”eh ina karantawa kai,
gaskiya novel d’in ya had’u. Farhat B
Haske tace” Queen Neenah n Khadeejat
kun karanta MARTABA TA da MATAR
MUTUM na Mrs Umar Soja kuwa?.
Sukace “a’a bamu karanta ba.
“Lalle an barku a baya ni harna gama
karantawa, yanzu ina karanta YAR
WAYE NE?.na Khairat S Panisau, da
KUDAN ZUMA na Zee Hrt.
Suka had’a baki tare da cewa”Farhat
littafin ya had’u ne?.
“Eh kai ana rikici kam, ku tamabi.
Hajiya Jamila Aliyu Haiydar tana dashi
sai ta tura muku.
Queen tace”Khady bari na nemomana
zan tura miki ina samu.
Khady tace”ok amma fa nagode. Farhat
B Haske tace”gaskiya ya kamata yanda
muka saba musan juna, gashi mun shaku
sosai, ae zumuncin bai kamata ya tsaya
a chatt ba.
Queen Neena tace” ae fa gaskiya kam,
yanzu musa rana sai mu fara zuwa
gidansu Khady.
“Ko ya kuka gani yan’uwa?.
Duka suka turo da haka za’ayi. Khadi taji
dad’i amma tana tunanin yanda zasu zo
Gwaggo zata iya cin musu mutunci.
Salama sukayi akan ran Friday za’a
had’u, a gidan Hajiya Jamila Aliyu
Haiydar sai su taho.
Gwaggo tana gama sake-sakenata tafito
ta kwala ma Khady kira, “fito dan
ubanki, mai fiska kaman na biri, kin
lashe wa mijina zuciya kin rabani da
yata, gashi kin samu d’an mutane, kinsa
yayi sata sun kawo kud’in aure ko?.
“To ni kam dai ahir d’inki.
“Kurwata kur bazaki iya ci ba.
“Ko uwarki ma haka tagaji ta barni don
nafi k’arfinku.
Nan take idon Khadi yaciko da kwalla.
Gwaggo ta tattaro wanke-wanke ta tara
mata, tashiga d’aki ta d’ebo kaya harda
wankaku, duk ta had’a mata.
“Maza-maza kiyi ki gama su yanzu, ki
kuma tabbatar an girkan abicin kar yayi
dare.
“Kin san halina basai an fad’a maki ba
aha.
“Ni ce Gwaggo Munguwa No1, in kika
kuskure min a aiki sai na miki ba dad’i,
tsohuwar mayya kawai.
“Mai son raba aure, amma kuma bazaki
iya ba sai dai a fasa naki.
“Kuma ina kan bincike duk randa na
gano gidan saurayinki, sai naje na had’a
duk wata manakisa ta, an fasa auren.
Niko Rash”nace Gwaggo rashin sani yafi
dare duhu, da kimsan Umar d’an waye
da baki fara masa rashin mutunci ba,
don yafi k’arfin raini.
Khadi ta dunkufa aiki baji ba gani, duk
da ta gaji amma bata son ta nuna bare
Gwaggo ta zagi iyayenta, don yafi komai
cin mata rai.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
’YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-111~115
Aiki sosai tayi, Gwaggo tana fita
makwabta, Beeba ta fito tafara tayata
aiki, Khadi tace”Beeba da kin bari nayi,
yanzu in Gwaggo tazo ta samemu, ni
zata zaga uwa ta uba. Beeba tace”karki
damu Adda yanzu zamu gama aikin,
Rabee’a ta fito sai mika takeyi, alamar
daga bacci ta tashi, kitchen ta wuce ta
duna tukunya, taga an kusa gama abinci,
kwano ta d’auko ta d’iba. Beeba
tace”Rabee wani irin iskanci kikeyi ne,
kina kalo muna aiki amma kizo ki d’ibi
abinci?. Baki ta murgud’amusu, Khadi
tace”kyaketa Beeba, kinsan Gwaggo na
dawowa saita huce a kaina. Aiki sukayi
cikin ikon Allah dake, duna da zafin
nama basu dad’e ba suka gama. Khadi ta
raba musu abin ci suka ci, Gwaggi na
dawoa tayi mamakin yanda Khadi ta
gama aiki da wuri, d’aki tashiga kwano
ta fito da shi, ta turo ma Khadi ga
wannan masaran kina gama cin abimci
ki surfa min shi, don yau surfen hannu
nake so bana inji ba. Cikin girmamawa
tace”to Gwaggo”.
A gajiye tayi surfe ta gama ta wanke ta
shanya shi.
Yau takama jumma’a yau ne su Hajiya
jamila da Queen Neenah zasu zo, yan
kud’in da ke Hannuta ta had’a ta siyo
kaya ita da Beeba sukayi girki. Ware
dubu biyu zata basu kud’in Napep, ta
gyara ko ina sukayi wanka ita da
Beebah, sunyi kyau sosai. Gwaggo na
ganin Khadi ta fito tace”mayya inda
kinga fiskanki da bazaki na yawo cikin
mutane ba. Rabee ta mata kalon sama da
kasa, sa’a d’aya Gwaggo bata sasu aiki
ba. Sai kusan karfe biyar, su Farhat suka
kira waya, Khadi ta d’auka da
“sallamanta kun isone?.
Farhat tace”eh! Gamu a dai-dai gun fire
servise”.
“Ok gani zuwa”.
Ita da Beeba suka fita, suna zuwa
kuwata gansu, da murna suka tari juna,
farhat tace”ikon Allah yau Allah yayi
zamu gana.
“Eh wallahi sannu ku da zuwa.
Su hajiya Jamila tace”wanna itace Beeba
ko?.
Khadi ta amsa da”eh! Itace, har kin
ganeta.
Suna hira suka shigo da sallama.
Gwaggo ta musu kalon sama da kasa,
Khadi ko sai addu’a takeyi, d’akin suka
kai su. “Gwaggo ta kwala ma Khadi kira”
ta amsa da “na’am gani zuwa”.
“Kee dan uwarki ina kika samu wayan
nan?. Ko maitan ki ya dawo har gida
kike lashe mutane?.
“Kiyi hak’uri Gwaggo kawaye nane fa”.
“Eyeh har wani daman kawaye kika
samu”.
“To yau zaku ci ubanku daga ke har
kawaye”.
“Dan Allah Gwaggo kiyi hak’uri ki bari
in sun tafi kimin duk abunda kikeso”.
“Kee ko uwarki bazata ban doka nabiba,
bare kee yar karamar kwaro”.
“Assalamu’alaikum Malam yayi sallama”.
“Khadi ta amsa”
Yana daga qofar d’akinsa
yace”Khadejatu! ”
Ta amsa da “na’am Baba”.
“Maza kizo nan”
Gwaggo cikin takaici ta ja tsuka. Sam
bata so haka ba, taso saita wulakanta
Khadi Malam ya dawo.
Da sauri Khadi ta nufi gun Malam, da
sallama tashiga d’akin, tsugunawa tayi
tace”sannu da dawowa Baba”
Cikin fara’a ya amsa da”yauwa d’iyata,
naji dad’in ganin ki, a cikin wannan
yanayi”
“Ya jinin yau fatan lafiya ko?.
“Eh! Lafiya lau, ga kwayena ma sun zi
gaida mu yau”.
“Ah madalla mun gode, in zasu tafi ki
fad’amin”.
“To baba”
Da Murna tayi d’akin ta nan tayi sannu
nasu Hajiya Jamila, Beeba ko har tayi
serving d’insu.
“Tace muje ku gaida Baba na” dukansu
suka mike har qofar d’akin Malam
sukaje suka gaida shi, ya sanya musu
Albarka. Gwaggo ma tafito daga d’aki
duka k’ara gaidata. A dakile ta amsa,
suka koma d’akin Khadi, hira sosai
sikayi, kafin suka mike zasu tafi don
magriba yayi. Ta d’ibi kayan kwaliya, da
sabulai, acikin wanda Dr Umar ya kawo
mata, da turaruka tasamusu a laida. Sun
fito Malam ya kirata yace”ga wanna
kibasu su hau adai-daita. Ta karba ta
“sukuma sukayi godiya”.
Har bakin titi suka rako su ta mika musu
tare da musu alkawarin zata zo ita da
Beeba.
Bayan kwana biyu Khadi na zaman
hak’uri, kulum da kalan horon, da
Gwaggo ke mata. Ana haka kwanwar
Gwaggo da yaranta suka zo mata kwana
biyu, kulum cikin kunci da matsi take,
itaji sanyi to tana tare da Malam ko
Beeba ko Dr Umar.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
’YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-121~125.
Gwaggo ta buga k’irji tace”nashiga uku,
anya kuwa ba Khadi mu bane.
Matar tace”nan gidan mana”. Innna
Yalwa tace”sannuku da zuwa ga gurin
zama”. Cike da fara’a suka k’ara
shigowa. Nan fa aka shigo da akwatuna,
ko da aka shin fud’a taburma, hmm
akwatuna bazai yiwu a bazasu, a tsakar
gidan ba. Inna Yalwa tace”yan’uwa yana
da kyau, kafin mu fara bud’e kaya, muyi
addu’a Allah ya sanya alkairi, ya kad’e
fitin-tinun dake ciki, ya kuma kawar da
idon mahassada da makiya, dazasu kawo
farmaki ma auren nan. Gwaggo tace”kee
Yalwa wa zaiyi hassda ko makiyi nasan
dani kikeyi, nan Gwaggo ta fara kwala,
ko ta kanta basu bi ba, sukayi addu’a
aka fara bud’e kaya. Yasalam masu
karatu karkuso kuga kayan yawanci
ready made ne, ga tsada, ko da ka zo kan
takalma duk gulma na, na kasa k’irga
yawansu, jakukuna da poss ba’a magana.
Ko da aka bud’e na d’ankunaye hmm
gwala-gwalai da fashion masu tsada, ga
manyan balguls ba a cewa komai, can
idona ya kyalo wani karamar a kwati
acikin kayan, da sauri Inna yalwa ta
d’auko, tayi-tayi ta bud’e amma ta kasa,
wannan matar ne tace”kawo ki gani,
tana tab’a qofar akwatin yafara k’ara
sauti mai dad’i gashi da k’arfi. Tana
bud’ewa yace Hello My Master, cikin
wata tausasashiyar murya na mata, kai
ka d’auka a fili mutum yayi wannan
maganan ba.
Wata mata da ke gefe, tace” a kula da
wannan a kwatin, don White Gold ne a
ciki, yana da matukar tsada sosai,
kud’insa ya kai miliyan uku a kud’in
9ja. Inna Yalwa baki har kuni godia suka
fara musu, sai suka d’auko d’an kayan
da suka had’a musu suka mik’a. Inna
Yalwa da dubu biyar a jikinta, ta k’ara
musu yadawo 15k. San suki karb’a sai da
su Inna Yalwa sukace”ko kun rainane?.
Da fara’a sukace”a’a Allah ya sanya
alkairi, wane mu da raina kyautan da
zata fito, daga gidan surkan Gwamna,
matar d’ansa d’aya tilo. Inna Yalwa
cikin rashin fahimta tace” umm Hajiya
bam gane kince Surkar Gwamna ba?.
Matar tace” eh ko bakusan cewa Umar
shine d’an Gwamna d’a d’aya tilo na
miji.
Inna Yalwa tace”sam bamu sani ba ya
ma b’oye mana ko shi waye”.
Take matar ta war-ware musu, aikafin ta
rufe baki. Gwaggo tasaka ihu ta hau
tsakiyar kayan tana watsi da su, tana
cewa” wanna fa k’arya ne d’an yankan
kai ne, Hajiya Suwaiba k’anwar Adam
Naira cike da mamaki, tace”lalle tabbas
yau naga halinki da’ake fad’a.
“Bari kiji ga kayan Lhadijat nan abu
d’aya ya bata sai mun miki rashin
mutunci, kisani duk wanda zakana masa
hassada da bak’in ciki, Allah kan masa
sakayya, mugunta da kike mata ne Allah
ta bata. Gwaggo tayi kanta zata
cakumeta wani security ya kaimata
naushi ta fad’i a kasa. Hajiya Siwaiba
tace”ae da ka barta da yau na koya mata
hankali, ni ba irin matan da suke
d’aukan wargi bane.
“Mtsss bamza sakarya marar imani.
“Khadijat takusa hutawa da muguntanki.
Gwaggo na ihu kamar mahaukaciya,
tana cewa”sai kun kawo na Beeba da
Rabee’ in ba haka ba zamana lafiya.
Gwaggo hauka tuburan Inna Yalwa ta
kali K’anwar Gwaggo tace”da fa kin
kama yar’uwanki kartayi tsirara, tsabam
bak’in ciki. Da kyar aka shigar da
Gwaggo d’aki aka kule ta.
Malam da yadawo, ko da yaji labari,
Hamdalah yayi, ya k’ara gode ma Allah,
tabbas Khadijat ta samu miji, don yana
jin labarin halin d’an Gwamna. Kayan
yasa ka aka d’eba a gidan aka kai gidan
Inna Yalwa da daddare, ba wanda
yasani, motar kuwa ya kai gun wasu
masu ajiye mota aka ajiye masa.
Yan’unguwa ko ina ka leka sai zance
akeyi, wasu ko so suke su ga Khadi matar
d’an Gwamna.
Gwaggo tana d’aki sai zage-zage take,
Beeba ko murna ba’a magana.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
’YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-116~120.
A gidan su Dr Umar kuwa, sun gama
had’a lefe nagani na fad’a, lefen nun ma
sa’a. Cikin kayan harda key d’in mota,
k’irar Honda CRV, Mum d’insa ta saka
masa, Dr Umar shima ya karo wasu kaya
aka saka, masu karatu kar kuso kuga
kayan akwatina ma Set hud’u akasa,
zannuwa kuwa ba kananu. Hmmm
kayan d’an Gwamna d’aya tilo aidole ya
zama abun kalo, Mum tace”Umar ka
sanar da Khadijat jibi za’a kai kaya.
Cikin murna ya shirya sai da ya je Store
ya mata sayya, ya nufi gidan, bai wani
b’ata likaciba ta fito. Sai da sukayi
hiransu yace mata”My Khady!”. Cikin
sanyin murya ta amsa da “na’am”.
“Khadijat! Duk wani farin ciki na kene,
ina matuk’ar qaunanki.
“Alhamdulilah! Allah ya amsa min
addu’a ta, na bani ke amatsayin mata.
“Ki sanar da mutanen gida, In Allah ya
kaimu jibi za’a kawo kayan lefe.
Cikin jin kunya ta saki murmushi, tare
da rufe fuskanta da tafin hannun ta.
Hira sukayi mai cike da so da qauna, sai
dab magriba, ya mata sallama ya tafi.
Khady na shiga gida ko da Malam ya
dawo, bayan ta masa sannu da dawowa,
ta sanar masa da sak’on Dr Umar. Cikin
farinciki ya yi musu addu’a.
Washegari Malam ya aika ma dangin
Mahaifiyar Khady, dangin Uba ya sanar
ma wayanda yakama ta su zo karban
kaya.
Malam ya sayo kayan karban bak’i,
harda yan kajin sa, guda biyar ya tura
kasuwan kauye, aka sayo masa. Ya sayo
multina da lakacera, kaya iya na talaka,
Baba Yalwa k’anwan Maman Khadi su
suka soya kaji, pepper meet sukayi, yayi
kyau ko ina sai kamshi yakeyi. Gwaggo
in banda harare-harare ba abinda
takeyi, ko hannu bata samusu a aiki ba,
karfe uku sun gama komai sun gyara ko
ina sai kamshi yakeyi. Malam yaje ya
d’an had’a kud’in da zai had’a na kasan
akwati, ganin karamci irin na Umar ya
samo dubu goma yaba ma Inna Yalwa
yace a basu. Khady ko tayi wanka cikin
kayan ta masu kyau, suka zauna a d’aki
ita da Beebah don basa son yawo.
Rabee’atu kuwa tana kusa da Gwaggo,
sai lashe baki takeyi, don tunda taga ana
soya kaji, yawunta ya kai.
Su Inna Yalwa wanka sukayi, suka saka
kayan su, mai kyau, suna zaman jiran
baki.
A gidan su Dr Umar kuwa, Mum kwanta
ta kira da matan Baba Liman, sai
Kwanwar Baban su Umar, bata tara
mutane ba, sabida tasan yanayin gidan
su Khady, kar suje su musu ba dai-dai ba.
Milasalin karfe hud’u da rabi, suka d’au
hanyan.
Misalin karge biyar, cikin unguwansu
Khady, ya d’au jiniya, motoci ne sukayi
jerin Gwano ga securitys a motoci sun
sanya sauran motan a tsakiya, suna
shigowa take suka fir-fito dan gani mai
zai faru. Motocin qofar gidan su Khady
suka tsaya.
Gwaggo dake d’aki taji jiniya mota,
tace”ko lafiya naji karan motar yan
sanda?.
Rabee tace”ai inaga wanda suka daki
Adda Khady ne suka dawo dukanta hala.
“Don ranan da irin wannan suka zo.
Gwaggi tace”Allah yasa sune, su dakata
inga ta inda za’ayi auren.
“Zo mu fita muga ya zasu kare. Suna
fitowa dai-dai lokacin yan sanda suka
shigo gidan da bindigansu, Gwaggo sai
zare ido take. ana haka suka ga wasu
Mata cikin shiga ta alfarma sun shigo.
Gwaggo tace”lafiya dai naga kuna shigo
mana gida?.
Wata mata mai yar kiba tace”nan ne
gidansu Khadijat?.
Gwaggo tace”eh! Nan ne.
“Lafiya dai?.
“Lafiya klau, kafin tayi wani magana
ansoma shigo da akwatuna.
Gwaggi tace”wanna fa?.
Matar tace”kayan Khadijat muka kawi”.
Gwaggo ta buga k’irji tare da zaro ido.
Nima Rash sai da wayata ta subuce don
na tsirata da ganin yanayin Gwaggo.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
’YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-126~130.
Hajiya Suwaiba suna komawa, suka
sanar da Mum d’in Umar yanda sukayi,
tayi mamaki sosai ashe da gaske haka
halin Gwaggo yake. Nan tace” hmm ni
gwanda His Excellency ma ya dawo ayi
bikin, yarinya ta huta.
Hajiya Suwaiba tace”yaushe zai dawo?
Mum tace” nan da 5days zai dawo. Hira
sukayi tayi da yanda biki zai kasance.
Gwaggi ko ta hana su Malam bacci sai
ihu take, ko sallah anki bud’eta tayi.
Khadi tayi murna tayi godia ma Allah da
zab’in da ya mata, take ta kira su Farhat
B Haske ta fad’a mata, Farhat ma take
bata labarin tayi sabon saurayi, Sunansa
Abdul-wasilu Humble, Khadi ta mata
fatan Allah ya dai-daita su.
Tana kashe wayar ta kira Queen Neenah
ita ta fad’a mata, daga nan takira Hajiya
Jamila Abubukar ta sanar mata, tayi
murna sosai da sosai, takuma bata
shawarwari da yanda zata kula da Umar
kasancewa Hajiya Jamila ta girmesu,
tana kwance dasune don taga suna da
hankali shiyasa.
Malam ganin iskanci Gwaggo zai wuce
gona da iri, da safe yaje ta windoq duk
ta wargaza d’akinta, yace”Hauwa ki
nutsu, wallahi kinji na rantse, matsawan
baki bar haukan da kike ba to yau zan
rubuta miki saki, don ba za’azo biki ina
matsayina na Surkin Gwamna a ga
mahaukaciya a gidana ba, kuma
haukanta akan bakincin take ma Surkan
Gwamna. Ni Rash nace”hmmm Malam
da biyu yayi maganan nan, don ya kuna
Gwaggo ne.
Gwaggo tace” eh dole kace haka ae dama
baka sona don yanzu kaga Khadi zata
auri d’an Gwamna dole kamin haka.
Malam yace” kene bazaki gane ba ina
sonki sosai, halinki ne bana so, ya fita
abunsa.
Gwaggo jin saki ta nutsu ko da tafito,
jummai k’anwarta tayi mata nasiha
tace”Yaya matsawan baki kwantar da
kai ba, ina fad’a miki zaki wahala don
yarinyan nan tayi gaba. Kiyi hak’uri
kawao.
Gwaggo tundafa wannan rana ta dawo
kamar bata gidan yanzu bata dai
magana da Khadi, amma ta bar
hantaranta ko sabganta tabar shiga.
Khadi ko kulum suna mak’ale da waya
ita da Umar, suna waya ne yace”gobe
Dad zai dawo ki shirya, in ya dawo ke da
Beebah zakuzo ku gaidashi.
Cike da murna tace”sai mun tambayi
Baba in ya barmu.
“Kedai nasan Baba bazai hana kizo ki
gaida Surkinki ba. Haka sukayita
hiransu mai cike da ni shad’i.
Washe gari da safe inna ta d’aura ruwa
a hita, dai-dai kusa da d’akinta a kwai
soket, ya tafasa ruwan ta kashe, taje
d’auko boket kenan ta sukuya tana
d’aurayewa, sai tebur d’in ya karye yana
shirin zubowa akan Gwaggo.
Khadi tafito da ga d’aki karaf idonta ya
sauka akan tebur, “kira ta kwala ma
Gwaggo, ganin bata gane mai take nufi
ba, da sauri tayi gun don ceton Gwaggo.
Tana zuwa ta ture Gwaggo ta hantsula
gefe kagin ta kauce ruwan ya juye mata
ajiki, wani razanane k’ara tasaki, ta
fad’i agun tana shure-shure. Gwaggo duk
ta rikice, Beeba da Rabee sai Jimmai
kanwar Gwaggo suma ihu suka saki, ana
haka sai ga Mal da gudu yayi kan Khadi,
wanda azaba yasa ta suma, d’aukarta
yayi waje yafita da gudu yashiga Napep,
Gwaggo ma da gudu duka bisa, Beeba
kam sai kuka take, tana fad’i”wayyo
Adda na!. Gwaggo sai hawaye takeyi,
tabbas yau Khadi ta gwada mata yar
halak ce ita, gashi taje ceton rayuwana
itakuma zata rasa nata. Tabbas yau na
yarda da kalman nan ta ‘YA’YA DA
DUKIYA BA’A K’ETARSU, bakan wanda
zai tai makeka ba.
Suna isa asibiti Dr Abdul suka samu
gani halin da take ciki, akayi Emergency
da ita, wayan Dr Umar yakira.
Dr Umar suna Airport shida Mum da
Ilham sunje d’auko Dad d’insu, don har
jirginsu ya sauka, Dad ya sauko kenan,
sun rungume juna, wayar Dr Umar tayi
k’ara gani Dr Abdul yasa yad’aga da
sauri “hello yace”.
Daga d’aya ban garen Dr Abdul
yace”kana ina, kazo ba lafiya Khadijat ta
kone bansam ko garin yaya bane, amma
ina zati ko Gwaggo nane ta konata
sabida halinta.
“What ina bazai yuba sai na d’au
mataki.
Mum tace”Kai da wa?.
Cikin muryan kuka ya fara basu bayani,
His Excellency yace” what muwuce
Asubiti yau matan na zata gane ita
bakomai bane.
Suna zuwa Asibiti ta ko ina ya amsa da
jiniya.
Dr Umar da Gwamna da gudu suka fita
duka shiga Emergency, Umar na ganin
halin da Khadi ke ciki, kara ya saki ya
fad’i sume. Mum da Ilham sai kuka suke,
Gwamna ya fita kiran Doctors suka d’au
Umar shima. Yana fitowa yaga su Malam
yace”ina Gwaggo da take?.
Malam ya nunata da yatsa, His
Excellency da gudu yayi kanta wani
damka ya mata, ya fara kwara mata
kyawawan mari, yace”wallahi in har na
rasa d’ana d’aya tilo, da abar qaunar sa,
to kema sai kinyi mutuwar wula kanci.
Kisani ‘DA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU.
amma ke munguwa nai bakin hali zaki
gane kurenki. Ball yakeyi da ita, yana
fad’an magan ganu, da kyar aka rik’e
shi, sijoji yace atafi da ita CID agana
mata azaba. Basu tsaya jiran komai ba
Women police suka d’au Gwaggi sama
aka sata a mota, aka nufi CID da ita.
Ni ko Rash tsaban gulma ina leka motar
naga bakin Gwaggo har ya kun bura,
fiskan taji marin manya, tamkar ba
Gwaggo mai bala’i ba.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[9:12PM, 9/14/2016] Rash Kardam:
’YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-136~140.
Umar kuka yake ana haka har suka iso
New Delhi, motane tazo ta d’aukesu har
asibitin da za’a mata aiki, kasancewa a
sanar musu, sun sanda suwansu, ana
shiga da ita likitoci, suka hau bata
taimak’on gagawa. Sun d’au awani suna
mata surgery, Umar ya kasa zaune ya
kasa tsaye, duka sun dun kufa sai addu’a
sukeyi. cikin ikon Allah likitan ya fito
cike da fara’a, hannu ya mika ma
Gwamna, yace’ In Allah ya yarda musa
tsamani komai normal”
Hamdalah suka rayi, suna gun akazo aka
wuce da ita zuwa d’akin da zasu ajeyeta.
Khadi bata far-fad’o ba sai kusan
3:00am na dare, doctors aka kira duka
dubata, Umat ko sai addu’a ke mata.
Haka suka kasance cikin jinyan Khadi
yau kusan watandu d’aya kuma yau ne
za’a ware mata, bandage, doctor
yace”suyi fatan Allah yasa aikin yayi
nan aka shiga da ita, wani room don
since mata, su Umar sai addu’a yakeyi.
Awa d’aya ya d’aukesu, likita ya fito nan
ya saida musu komai normal, zasu iya
shiga su ganta, Umar da gudu yayi
d’akin yana zuwa ya ganta kwance, suna
had’a ido murmushi ya sakarmata, zuwa
yayi ya rungumeta, ana haka su Malam
suka shigo, sai da Dad yayi gyaran
murya, tukun ya san sun shigo, cikin jin
kunya ya koma gefe, sannu suka ringa
mata.
Tun daga wanna ranan Umar shike mata
dressing d’in ciwonta, ya bata abinci
abaki, ya mata alwala, da daddare kuwa
kafin ta kwanta zai d’auko story book
yana karanta mata, da joke masu dad’i
tana dariya, har tayi baci, inyaga tayi
nisa da bacci yazo ya ru gume matarsa
haka rayuwansu, ya kasance gwanin
dad’i. Ganin Khadi ta warke suka fara
ahirin dawo 9ja don ayi biki kowa ma
ya huta.
Gwaggo kam taci a zaba, in har kasanta
ada kaganta yanzu bazaka ganeta ba,
tayi baki sosai, gashi har hak’urinta sun
zube, tsaban duka da wahala, sai daga
baya ne, Beeba ta sanar ma Dr Abdul
gaskiya, shima ya fad’a ma Baban Umar,
sai da sukayi bincike suka tabbatar da
gaskiyan al’amarin kafin aka saketa,
randa tashiga unguwansu, matasa suka
tashi zasu mata duka da kyar aka
kwaceta, Gwaggo tayi nadama ba kad’an
ba. Kulum cikin saloli take, tana addu’an
Allah ya tashi kafad’un Khadi.
Yau jirgin su Khadi ya sauka 9ja, Umar
ko sai wani rawan kai yakeyi, ko
kunyasu Dad baiji, sai yawani rok’o
hannuta, sai da Mum ta zo ta rik’e
hannu yarta, Mum tace”Malam za’aban
aron yata, zan tafi da ita kafin biki.
Yace”bakomai ae Khadi takune.
Suna isa gida ta kira Hajiya Suwaiba da
Ameena tace”ga yata nan kuje a gyara
min ita, banson Umar ma ya ganta sai
biki.
ﺭﺷﻴﺪﺓ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﻛﺮﺩﻡ
[4:55PM, 5/25/2016] Rash Kardam :
’YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU
NA
©RASHEEDAH .A. KARDAM.
Pg-141~145.
Shirye-shirye biki akeyi ba sanya, su
Hajiya Jamila.k’irjin biki, su Farhat da
Queen Neena takanas suka koma gidan
Hajiya Suwaiba da zama, abunda aka
shirya za’ayi ran Alhamis kamu, sai
Jumma’a Walima da daddare kuma
dinner, washe gari asabar yini. Komai
ya tsaru yanda ake so, yau ne ranar da
za’a fara Kamu, da yamma ko kwaye sun
shirya, har an kaisu gun jiran isowar
Amarya ake, ba’a dade ba kuwa ta iso
cikin wata lafiyayiyar mota, tun dana
zuba ido ma Khadi kasa d’aukewa nayi,
gaskiya tayi kyau, duk yan guri sai yaba
kyanta suke, taro yayi taro, komai yatafi
yanda akeso, sai kusan shida suka gama
kamu, daga gun gidan, Hajiya Suwaiba
aka sake kaita.
Washe gari akayi walima shima tsaru
daddare kuwa sukayi shirin dinner.
Hajiya Suwaiba ta bada umurni akai
Amarya gidansu daga can za’a wuce da
ita Dinner har a kaita gidanta, wannan
umurnin Mum ne.
Masu karatu in bakwayi bamu guri,
tundaga nesa na hango motoci jere suna
d’eban mutane, sai da aka gama diban
kowa, na hango wata maroon d’in lemo
zeen ta perker, su Gwaggo da’ake leke,
baki tasaki tana kalo, don tunda take
bata tab’a, ganin irin motarba. Nan
akace afito da Amarya Inna Yalwa ce ta
rakota, ohoho sunan wani kalma waishi
sorry!! Masu karatu karkuga Khadi, in
har nace zan iya tsara muku kyan da
tayi, wayana ba zai d’auka ba. A hankali
suka isa jikin motar tashiga, ana tayar
da motan taji an rik’o hannuta, a razane
ta juya Umar ne yaaha kyau.
Koda suka isa gun dinner duk wanda ya
gansu sai ya yaba, haka taro ya kare
kowa cike da murna.
Da safe Malam ya kira Khadi, ya mata
nasiha, yan’uwan Mamanta suma nasiha
suka mata, Gwaggo da k’afarta tazo tana
kuka ta roki Khadi yafiya, Khadi tace”
ba komai ta yafe mata.
Da daddare aka d’au Amarya sai gidan
Umar niko Rash nace”fatan alkairi.
Gwamna gida mai ji da kyau ya bamasu
Mala
adsense 2 here