Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, September 4, 2017

Billy pinky durlin complete

adsense here

[9/22, 5:36 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [7/26/2016]
*👛BILLY PINKY DURLING*👛


*Na*
 *Billy giro😊*


*Page*
*👛1 & 2 👛*
  *I* hate u!
*I* hate u!! *I* am absolutely hate u *Bobby!!*bagidaje kawai wanda bai san abinda yake ba!....ke! ni kike gaya ma haka! Eh na fad'a kai baqauye  ne,kana ikirarin ka waye  amma kana abubuwan qauyawa,bari in gaya ma kai baqauye ne ko baqauye kuwa na qarshen qarshe domin duk wayeyyen mutum bazai ta6a sa ido akan abinda wani  keyi ba wlh!da har zaka zo kana takura ni akan ra'ayi na!hakan yasa naji na tsane ka a rayuwa ta!
   Gabadaya gayen yaji duk ta halaka shi domin da ka kira shi baqauyen mutum gara  ka same shi ka masa dukan tsiye har ma ka had'a da zagin iyayen sa da kaf danginsa hakan ya fi masa da kace mishi baqauyen mutum.
  Wani  irin 6ari jikin sa keyi idanuwan sa sukayi jajir sbd tsananin 6acin rai yace"ke ni kike kira baqauyen mutum.... qarya nayi dube ka fa! Ta fad'i haka ne yayinda take kallon shi sama da qasa a wulaqance,
 wanda ni Billy giro a iya gani na gayen ya bala'in waye wa kuma ya had'u ta ko ina baya da makusa domin da waye wa da kyau kesa a shiga Aljannah sae dae nace yayi sa'a.

   Amma ita kallon shi take cike da tsana qarara a idonta yayinda take qara ganin shi baqauye bidib.
    Tace lemmi tell u one thing, wlh bobby da saman ka har qasa kallo daya za'ayi maka a gane cewa kai baqauye ne na qarshe na fad'a!.....wani  irin wawan mari ya kife ta dashi ta saki ihu sosai duk gidan ya kar6a, da sauri wata mata ta fito tace"me nake shirin gani Hakeem ba dai qanwar taka ka mara ba,yanxu har fadanku ya fara kai ka da dukan qanwar ka,,gwaggo wlh idan ta sake kira min wannan kalmar da take fad'a min sae na mata dukan tsiya... Kai Hakeem qanwar kace fa ka daina biye mata yarinya ce.......Ki bashshi gwaggo ba dukan tsiya zai min ba ya kashe ni idan zai iya,amma ni bazan ta6a daina ce masa baqauye ba!
      Nace kai baqauye ne na qarshe,na fad'a ka kashe ni!.....rufe bakin ta keda wuya taji saukar mari,ihu ta saki mai had'e da kuka tace wlh bazan daina ba sae dae ka kashe ni,nace kai baqau......wacce suka kira da gwaggo ce ta rufe mata baki,wanda yayi dai dai da isowar wata mata, cikin 6acin rai matar tace"Hakeem ban hana ka ba,wai me ya
sa baka jin magana!nasha gaya ma ka fita harkar 'yata!ran Hakeem ne yayi mugun 6aci domin ya tsani ayi masa fad'a a gaban mutane!yace "umma kinji me take ce min kuwa,a commonn Stupid girl irin ta zata kira min wannan kalmar.....ka fara kira ma kanka stupid kafin ka kira ma wani!...wai baza kiyi shiru bane billy,keda ma ba kya tanka masa meyasa yau kika tanka masa? Wlh mama ya ban haushi ne kullum ya cika takura ni wai me kala d'aya, mai kala d'aya me ye ruwan sa da ra'ayi na, ni naji ina ra'ayin pink colour ba wanda ya sani, shine wai yau don nasa an canza min mota ta to pink colour ya hana a shigo da ita gidan nan kuma yasa aka qona min ita..... What! motar taki da aka siya jiya jiya? Eh mama tayi" maganar ne cikin muryar kuka.

Mamar ta kalli Hakeem da mamaki tace"Hakeem lafiyar ka kuwa!kallon mamar yayi ya d'an kauda kansa gefe yace"mama wai ba ku ganin dabbacin da takeyi ne komai nata pink colour har ma ace duk garin nan ba wanda bai sani ba,wannan wace irin jaraba ce da hauka! Kuma ko cikin kaloli bata ga colour din da take so ba sae pink,bagidajiyar kala.... To Hakeem ina ruwanka! ra'ayin ta ne... Hm mama ki barshi tukun yaje ya kalli madubi idan yaga kansa da kyau sannan ya iya dawo wa yaci gaba da inda ya d'ora,cike da tsana Hakeem ya kalle ta ya buga tsaki tare da "fad'in er iska kawai mai kala d'aya" yana gama fad'a ya fita,Billy ta ya mutse fuska zuwa kuka sbd kiran ta da yayi er iska.
    Fadawa tayi jikin mamar tana kuka cike da shagwa6a ta d'ago idanun ta da suka cika tap da hawaye tace"mama kin ji shi ko"yi haquri zo muje daki shi da Abban shi ne yau ba mai raba su.


Hakeem kuwa yana shiga d'aki ya cire kayan sa gabadaya komai bai bari a jikin sa ba, yayi musu kallon d'ai d'ai,bai ga ko dot d'in pink a tare da kayan shi ba,
 tsaki kawai ya buga ya wuce toilet ya watso ruwa ya fito yayi zaune kan mirror yana qarewa kansa kallo domin yaga shin ina ne pink yake a jikin sa domin ya hanzar ta cire shi, haka ya qarewa kansa kallo baiga pink ba,nan ma tsaki ya buga yana mai jin haushin kansa yace"meyasa zan 6ata lokaci na,na yarda da maganar wannan dabbar,tashin da zai yi ne sae ya tsaya cak yana qarewa fuskar shi kallo har dai lips d'in sa, a hankali yakai hannu ya murza lips din shi, da sae yau ya ta6a fahimtar pink ne,wani  irin tsanar kansa yaji,cikin d'aga murya yace"No!!!!nan yayi watsi da duk turakkan da ke kan mirror, na fashewa suka fashe wad'an da basa fashewa suka shiga yawo a tsakiyar tiles.

  Nan ya shirya a gaggauce ya figi motar sa ya fita bai zarce ko ina ba sae *HAKEEM SPECIAL HOSPITAL*
Da shigar shi mutane sae bashi hanya suke sbd gudun kar ya bangaje su.
   Office d'in wani  doctor ya nufa ko sallama bai yi ba yace"Amjad kasan me ya kawo ni!?ya nuna lips din sa yace "pink lips d'in nan nake so ka canza min su koma irin na kowa,da mamaki Amjad yace"Hakeem wannan fa halitar kace ba yanda za'a canza ta... Kai dai ne baka san yanda zakayi ba ko kuma nace baza a iya yin hakan a qasar nan ba,gobe ya zama dole na bar qasar nan zuwa New delhi domin amin plastic surgery a canza min wanan pink lips,,,
 me yake damun ka ne Hakeem,Amjad idan ba a canza min pink lips d'in nan ba bana jin zan sake son kai na,Amjad zan iya kashe kaina idan har nayi sati da wannan abun,bai jira me amjad zai ce ba ya fita yabar Amjad cikin tsananin mamaki.

 A 6angaren Billy kuwa Abban yana dawo wa ya shiga lallashin ta kan ta kwantar da hankalin ta indai mota ce, yau d'in nan zata yi sabuwar mota dal domin yanzu haka motocin da Hakeem yasa aka yo masa order sun iso ciki taje ta za6i d'aya son ranta,ya fadi haka ne yayinda ya bata keys.
   Nan Billy ta qanqame baban tace"thank u dad!

Hakeem kuwa yana fitowa asibiti ya zo gida, koda ya shigo harabar gidan sae kallon sabbin motocin sa yake guda biyu black & white sae dai kamar yafi son baqar domin yafi kallon ta.

Yana shiga falon yayi dai dai da billy ta tashi zata je ta za6i d'aya daga cikin motocin da aka ce ta za6a.

Abba yace "yayi kyau Hakeem! naji duk irin izgilancin da kayi don haka kasani izgilancin da kayi zai koma kanka,domin mamana zata za6i d'aya daga cikin motocin da suka iso yanzu... Pls Abba wlh ina son mota ta,kasan cewa dayar ta Amjad ce,kuma Abba kasan irin yanda aka wahala kafin a sami dayar, Hakeem wannan karon bazan lamunta maka  abin da kake yiwa mamana ba,,,ni gasky Abba sae dae na biya ta kudin motar ta amma baza ta dauki tawa ba.

Billy najin haka ta sace jiki ta fita sae da ta qare ma motocin kallo sannan ta nufi dakin mai gadi ta dauko galan ta nufi baqar mota wacce iya haduwa ta hadu har ma takai qarshen had'uwa,
Billy na zuwa ta shiga motar ta maida ta dai dai tsakiyar gida,ta fito riqe da galan wanda nake tsammanin fetur ne a ciki, tabi koina na motar ta zuba.

Sae ga Hakeem ya fito ya same ta tana aikin,ta kalle shi fuska ya mutse tace "dama  kuwa a gaban ka nake so na aiwatar da abin da nake shirin yi yanzun,idan kai ka kasa yi a gabana ko kuma ince kasa wasu sukayi sbd tsoro to ni da kaina zanyi kuma  a gaban ka!

Hakeem bai ce mata komai ba sae kallon ta yake a wacce ta zautu don ganin yake ko giyar wake tasha bazata qona masa mota ba asali ma ya dauka ruwan banza ne ta sakawa motar.

 Taci gaba da cewa"Bobby na yaba sosai da yanda Abba yamin,wato hukuncin da ya yanke, amma sanin kan ka ne duk wani  abu da ya fito daga hannun ka ko ya fito da sunan ka na tsane shi bare har na iya zama da shi a matsayin nawa, shiyasa zan yanke hukuncin da nake ganin shine dai dai a gurina, tana gama fadar haka ta qesta ashana ta cinnawa motar wuta, sannan ta jefa masa key tace"go and save ur motor if u can"ta wuce ta bar shi tsaye sororo yana kallon motar sa naci da wuta wanda ji yake tamkar zuciyar sa ce ke ci da wuta.

*Billy giro😊truncated by WhatsApp]
[9/22, 5:39 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [ 7/27/2016] Billy giro😊:

*```👛BILLY PINKY DURLING👛```*



*Na*
*Billy giro*😊

*Page*
     *👛3 to 4👛*
Billy na shiga falo ta fad'a jikin Abba cikin kuka,Abba yace "mamana lafiya kuma me yake faruwa ko ya kar6e makullan ne? dagowa tayi cikin kuka hawaye sha6e sha6e a kumatun ta har suna diga kan rigar ta,tace"ba makullan ya kar6e ba Abba motar da na za6a ce  yaje ya saka mata wuta ina ciki domin ganin lafiyar motar ban ankara ba kawai naga motar ta fara ci da wuta wanda da yanzu dani ciki ba don nayi saurin fitowa ba,"innalillahi wa inna ilaihi raji'un! cewar umma, Abba kuwa cikin tsananin 6acin rai ya tashi ya nufi hanyar fita sae ga Habib ya shigo rai 6ace ya nuna Billy yana qoqarin yace wani  abu Abba ya kife shi da mari biyu masu kyau wanda duk tsananin girman falon sae da ya kar6a "abinda ba'a ta6a yiwa Hakeem a rayuwa ba wato mari, hakan yasa ya shiga mamaki muryar shi na rawa yace"Ab..ba me kuma nayi?..... "ba Kaine ka qona motar da na za6a har ma kana qoqarin hadawa dani" cewar Billy wacce ke jikin umma tana kuka kamar da gaske, Hakeem kam kasa cewa komai yayi sbd imani ne ya masa yawa, zafi uku uku a lokaci d'aya wanda nan take idanuwan shi sukayi jajir suka ciko da qwalla,sbd wasu maganganu da yaji umma na fadi"Hakeem sae yau na tabbatar da cewa na haifi d'a ban haifi halin sa ba wanda har fargaba nake idan ba canje aka min a asibiti ba!
Abba yace" tabbas Hakeem na kusan kawo qarshen qiyayyar da ke tsakanin ka da mamana....Abba.. Ka 6ace min da gani shàshan yaro kawai!bai fita ba sai da yayi ma Billy wani  irin mugun kallo, yayinda ita ma ta watsa masa shu'umin kallo.

Nan su ka fito domin ganin motar, hayaqi ne baqiqirin har bakin qofar falon duk da irin nisan da ke tsakanin su da motar sbd gidan mai fad'i ne sosai.
   Nan take Abba ya kira motar kashe wuta suka zo suka kashe tare da fitar da motar,nan aka sa masu aiki suka gyare harabar gidan tsaf kamar ba abinda ya faru.

Sannan Abba ya samu natsuwar lallashin Billy har ta daina kuka ta tashi taje d'aki tana mai jin farin ciki fal a ranta.

Hakeem kam baqin ciki ne ya masa yawa domin tun lokacin da yaje 6angaren sa ko fitowa bai sake yi ba har safe.

Da safe Billy ce ke saukowa a hankali kan staircase yayinda take dauke da pink dress riga da wando dai dai jikin ta rigar dogon hannu ne da ita a qasan gefen wandon kuma akwai wata er pink flower da ke dauke da duwatsu biyu dake reto a hankali, flat shoes ne  sanye a qafar ta kasancewar billy yarinya ce mai tsayi shiyasa high heel basu dame ta sosai ba.
   Fuskar ta na dauke da er simple makeup,tana sanye da glass kanta kuwa d'an qaramin gyale ne tayi rolling dashi yayinda jelar gashin ta ke reto a baya,gabadaya jikin ta ba abinda zaka nema ka ganshi a wata kala face pink domin kuwa ko phone din da ke hannun ta pink ce,key holder motar ta ma haka,bcs riqe take da makullin mota da alama fita zata yi.


Murmushi ne ya bayyànà a fuskar ta ganin mutanen da ke zauñe a falo, Abba ne zaune shida wani,cike da murna ta qarasa gurin wannan mutumin ta rungumo shi a hankali tare da d'ora mishi peck a kumatu tace"Abbana yanzun kazo"cike da murmushin dattijan taka yace"yanzu nazo mamanah,ya akayi ina zuwa haka?a shagwa6e ta kalle shi tace"Abba gurin ka zanje mana sae gashi kazo,,to yi haquri mamanah,nazo ne domin magana zamuyi dake da yayanki Hakeem zauna ki jira fitowar shi.
   Nan ta zame jiki ta zauna qasa ta jingina a jikinsa ta dora kanta a qafafun sa tana tambayar sa ya hanya da mutanen da ya baro, amsa yake bata yayinda yake shafar gashin kanta.

Ba jimawa Hakeem ya shigo sae da ya gaishe su sannan ya nemi guri ya zauna ba tare da ya kalli gefen da Billy ke zaune ba haka ita ma kamar ma bata san da shigowar shi ba.

Abba ya gyara muryar sa zai fara magana wayar shi ta shiga ruri,ya dauki wayar bayan ya gama ne yace da su"ina zuwa"

Nan ya fita ni Billy giro nace to bari na d'an baku taqaitaccen labarin yanda familyn yake.

Alhj Qasim da Alhj Mansur en uwan juna ne na jini domin kuwa ciki d'aya suka fito,asalin su en shuwa Arab ne, Alhj qasim shine Babba sannan Alhj mansur,kowanen su na da wadata domin ba wanda zai nuna ma wani dukiya a cikin su.

Alhj qasim yana da mata d'aya wato Hajiya Aisha suna da d'ansu d'aya wato Hakeem.

Alhj mansur shima matar sa d'aya  hjy maryam wacce garin haifuwa ne ta rasu bayan ta haifo santaleliyar 'ya jawur da ita mai kyaun gaske,wacce taci sunan kakar ta wato Bilkeesu shiyasa suke kiran ta da "Mamana"
   Ganin mahaifiyar Bilkeesu ta rasu ne yasa Alhj qasim ya d'auki Bilkeesu ya maida ta gidan shi inda Hajiya Aisha ta d'auke ta tamkar er ta, madara Billy ke sha kasancewar Hajiya Aisha bata da ruwan nono bcs ta jima sosai da yaye Hakeem domin a lokacin kusan shekarun sa 7 kuma basu yi tunanin tasha wani  magani ba ko zatà sami ruwan nono sbd Bilkeesu tana shan madarar ba wasa .
   Duk da Alhj mansur ya sake aure baisa ya dauki er sa Bilkeesu ba.
   Gashi Hakeem baya qaunar ganin umman sa riqe da Bilkeesu,kasancewar sa yaro ne mai kishin ganin mahaifiyar sa riqe da wani yaro ba shi ba,
 shine fa tun daga lokacin tsanar Bilkeesu yake,ba Bilkeesu ba ma komai indai nata ne to ya tsane shi,idan kuwa yaga Bilkeesu da irin kayan shi ya rabu dashi har abada ba zai qara waiwayar sa ba, wanda hakan tsanar taci gaba da qaruwa har zuwa girman su haka yasa ita ma Bilkeesu ganin tsanar da yake nuna mata taji duk duniya ba wanda ta tsana kamar shi,da duk wani abu nashi.
    Akan tsanar da suke yiwa juna har en aiki suka raba,wato kowa da wanda ke masa aiki,
gwaggo ita ce mai aikin Hakeem,Billy kuma wata yarinya ce mai suna Baraka.

    Iyayen su basu ta6a tsammanin haka qiyayyar zata ci gaba ba, sun d'auka cewa a iya yarinta zata tsaya,sae gashi har girman su, shiyasa yanzu abin yake matuqar damun su sosai,har dai da suka kasance su kad'ai ne 'ya'ya a gurin su.

Kuma Hakeem ya qara tsanar Bilkeesu ne bcs of kala d'aya wato pink colour da take mutuwar so tun tana yarinya, iyayen kuwa suka biye mata duk abin da zasu saya mata pink colour suke saya mata,tufafin ta pink,takalman ta pink,underwears pink, haka ma dakin ta har zuwa toilet duk da pink akayi mata qawa,to fa akan haka ne Hakeem ya tsani pink colour kasancewar ta choice d'in Bilkeesu, shiyasa ko cikin gari ya shiga ba yason gani wulgawar pink colour ta koina.
 
Hakeem yayi karatun soja ne a qasar turawa,inda en mata ke son shi sosai sbd kyaun sa bai ta6a kula kowa ba sae mace d'aya,da ake kira Jennifer rayuwa da Jennifer ne yasa Hakeem bai d'auki ta6a jikin mace a komai ba,hug da kiss kuma ya d'auke su tamkar gaisuwa,wanda har akwai wani  lokaci da ya dawo daga karatu, Jennifer ta kasa haquri ta biyo shi har Nigeria agaban su Abba, Hakeem yaje ya rungume ta ya mata kiss.

Akwai kuma wani  lokaci da Jennifer taje 6angaren Hakeem ta same shi ya fito daga wanka, ga Hakeem mutum ne wanda tun a toilet corner yake goge ruwan jikin sa hakan yasa ba ya fitowa da towel sae dae ya fito hakan nan ba komai a jikin sa.
   Nan Jennifer ta qarewa hallitar sa kallo wacce ta rikitar da qwaqwalwar ta,sae gabadaya sha'awar shi ta taso mata, da yake dama ta jima tana sha'awar Hakeem amma bata ta6a samun damar sa ba.
   Kallon sa take tayi Hakeem bai san tanayi ba bcs bai ko lura da mutum a d'akin ba sae jin yayi an rungumoshi tana masa wasu irin rikitattun abubuwan da ya kasa fizgar kansa da sauri,sae ga Billy ta shigo d'akin tana qwala ma jennifer kira,nan Hakeem ya ture Jennifer da qarfi ya nemi abu ya rufa jikin sa, Billy kam tuni ta bar dakin yayinda tsanar Hakeem ta qara ruruwa a cikin ranta.
 
Hakeem kuwa dukan tsiya yayi ma Jennifer ya kuma kore ta daga gidan.
   Wannan kenan a 6angaren Hakeem.

A 6angaren Billy kuma
*Billy pinky durling*shine sunan da qawayen Billy ke kira mata a school,kuma wasu kan kira ta da"Billy pinky ko pinky durling,ko pinky wasu kuma  Billy suke kiran ta kamar yadda ake kiran ta a gida.
   Billy ta kasance yarinya,wacce kwata kwata bata da girman kai shiyasa maza da mata en school d'in su duk shiri suke da ita, har ma suna  kai mata ziyara a gida akai akai sae dae maza sunfi zuwa sosai, wanda ko ba kowa a gidan takan kai su main falo ta kawo musu abin motsa baki,su zauna suyi ta fira suna nishad'i,hakan yasa Hakeem ke kiranta er iska domin ganin yake shigar da takeyi da maza a main falo kuma ba kowa a gida, ba komai sukeyi ba face lalata har ganin yake kaf samarin garin sun santa a matsayin "ya mace.

Wannan kenan.
 
Ci gaban labari.

 Sosai Abba ya jima kafin yake dawo wa da alama baqo yayi,
    Zaman sa keda wuya ya fara da cewa"Hakeem,mamana ina so ku bani hankalin ku domin kuji abinda zan fad'a da kyau, a gaskiya qiyayar da kuke nunawa junan ku bata mana dad'i ko kad'an har ma mutanen waje na tunanin kodai ku ba en uwan juna ba ne, jin hakan yana qara qona min rai sosai,wanda a kullum addu'a ta ita ce Allah ya nuna min ranar da kuka daina nuna qiyayya wa junan ku,najima sosai ina wannan addu'ar kuma ina ji a jikina Allah zai amshi roqo na.
   Hakan yasa muka kira ku domin sanar da ku hukuncin da muka yanke wanda ba mun yanke shi bane don mun kasa haqurin jiran hukun cin unbangiji, munyi haka ne don kawo karshen qiyayyar da ke tsakanin ku.


   Hukun cin da muka yanke shine a cikin satin nan idan Allah ya yarda zamu had'a ku aure ma'ana  kai Hakeem zaka kasance mijin mamana, ke kuma mamana zaki kasance matar Hakeem!

*```Billy giro😊```*
®NAW✍[truncated by WhatsApp]
[9/22, 5:44 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [7/28/2016] Billy giro😊

*```👛BILLY PINKY DURLING👛```*


*```Na```*

*```Page```*

      *```👛5👛```*
zumbur Billy da Hakeem suka miqe cikin tsananin rud'u!kya rantse da Allah mutuwar iyayen su aka sanar da su.

*```Hakeem```* ya tashi ne tare da dafe kunnuwan sa yana mai fading"innalillahi wa inna ilaihi rajiu'un! da banzo duniya ba da banji wannan mummunan labari daga bakin ka ba Abba.

 *```Billy```* ta tashi ne tare da cire glass din idon ta tana mai fad'in innalillahi wa innailaihi raji'un,Allahumma ajurni fi musibati wa ahlif lee khairan minha!na shiga uku!Abba wannan wane irin hukunci ne haka.

Sun fara maganar ne a tare suka sauke ta a tare.

 Abban Billy ya kalle ta da mamaki yace"mamana addu'ar me nake ji a bakin ki sae kace wacce ta had'u da wata masifa... Wlh Abba  abin da naji ya ma wuce masifa a gurina,wanda har ma na tsinci kaina da son ace nayi zamani na a cikin zamanin da suka shud'e da kwata2 ban ma san waye Hakeem ba,don girman Allah Abba ku daina wannan zancen wlh na tsani Hakeem!
 na tsani ko ganin sa Abba"tana maganar ne wacce kalo d'aya zaka yi mata kasan cewa ta rikita sosai da jin zancen,
 domin hawaye sae kwarara suke a idonta yayinda ta durqusa akan guiwoyin ta tana roqon mahifin ta,
wanda ya dakatar da ita cikin tsawa Yace"mamanah!! ban hana ki fadar wannan kalmar wa d'an uwanki ba!
Sautin kukan ta ne ya fito sosai ta tafi da gudu ta haura sama zuwa d'akin ta.

Hakeem kuwa mari mahaifin sa yakai  masa yace"Hakeem yanzu ni kake gaya ma cewa nazo ma da mummunan labari!
    Hakeem kam tamkar wanda bai ji marin ba ko kuma ince har fad'an da Abba ke masa bai ji ba domin sae qara dafe kunnuwan sa yake yana ta faman maimaita innalillahi wa inna ilaihi raji'un! kyace wani abu mai ciwon gaske ke yawo a cikin kunnuwan sa alhali maganar Abba ce ta hukuncin da suka yanke keta masa yawo a kunne,
 nan ya fita kamar wani  zautacce ya nufi 6angaren sa.

 Yana shiga d'akin sa yayi kici6is da kayan sa da ya shirya domin zuwa new delhi, qafa yasa ya shure kayan domin kwata kwata kansa ya kunce bata zancen zuwa New delhi yake ba sae qoqarin yake wannan kalmar ta daina masa yawo a kunne ko zai samu ya farka daga mummunan mafarkin da yake,bcs shi haka ya ajiye abun a mafarki.

Billy kuwa tana shiga daki ta fad'a ruf da ciki kan bed tana mai rusar kuka.


 Cike da 6acin rai Abban Billy ya bar gidan haka ma Abban Hakeem ya tafi d'aki yana mai jin baqin cikin wannan qiyaya ta 'ya'yansu da kullum sae qaruwa ta ke.


Haka gidan ya yini ba dad'i Hakeem da Billy tunda suka shige ba wanda ya fito a cikin su har dare, umma ba yanda ba tayi da Billy ba akan ta bude d'aki amma taqi sae sautin kukanta da ake ji.

Wasa wasa har safe Billy da Hakeem ba wanda ya ko leqo.


  Guraren qarfe goma na safe Hakeem ne ya kammala shirin sa tsaf na zuwa new Delhi ya dauki duk wani  abu mai muhimman ci a gurin shi,
aikin sa yake  kamar wanda bai kwana a cikin  damuwa ba.
   Ya dauki makullin motar sa kenan wayar sa ta shiga ruri,sunan Dad ne ya bayyana a screen ya daga wayar hade da mishi ina kwana,sannan yace gani nan zuwa.

A main falo ya nufa ya shiga da sallama, ya gaida Abba da umma da ke zaune,umma ce ta amsa Abba kuwa tamkar bai ji shi ba.
    Qoqarin zama yake Abba yace "kar ka zauna je ki ra min mamana,kuma ka jira sae kun zo tare,rai 6ace Hakeem ya haura sama yana tunanin ina ma ne  sabon d'akin ta da ta koma wanda yau watan ta biyu kenan da komawa,amma Hakeem bai san dakin ta ba, jikin qofa ne ya bashi damar fahimtar d'akin ta,
 kasancewar sa pink colour,wanda akayi ma kwalliya da fararen duwatsu kamar diamond.

Knocking ya shiga yi har ya gaji ba alamar za a bude Billy naji amma ta share ba wai don tasan wanda ke knocking ba sae don sanin dakin a bude yake,kuma bata jin zata iya tashi.

Tsaki ya buga had'e da murd'a qofar sae kuwa qofar ta bud'e,
 a hankàli wani  irin qamshi mai dadi had'e da sanyin Ac suka ratsa shi.
Hakeem ya 6ata fuska yayi shiru kamar mai tunanin wani  abu,can ya daure ya watsa idonshi a cikin dakin ya hango ta kwance kan bed kamar wata baby doll(er tsana)tayi ruf da ciki tana sanye da er fincikar rigar baccin ta pink wacce ta d'an yi fitting d'in ta,rigar mai dan siririn hannu ce iya cinya wanda hakan ya bayyanar da santala santalan cinyoyin ta,masu sheqi,
 gashin kanta duk ya baje akan pillow har zuwa gadon bayan ta, komai baya motsi a jikin ta ma'ana kamar mai yin bacci,hannun ta da take shafa qatuwar teddyn ta ne zai baka damar cewa a farke take,amma kwata kwata bata nuna alamar cewa taji an bude dakin ba duk da kuwa taji, cike da qyama Hakeem ya kauda idon shi yace "kizo Abba na kira"
  bai jira me zata ce ba ya tafi abin sa.

 Bata 6ata lokaci ba sbd jin wanda ke kiran ta, hakan nan ta fito bata damu da rigar da ke jikin ta ba,tazo ta sami Hakeem yana jiran ta,
 bata bi ta kansa ba ta fice,umma ce ta fara hango ta,fuskar ta fayau da gani taci kuka, kuma har ta rame lokaci d'aya kamar wacce tayi sati bata da lafiya, bare dama ko banza Billy sililiya ce,tana qarasowa ta gaida su ta samu guri a qasa ta zauna,shima haka Hakeem.
   Abba ya kalli Billy yace"mamana je ki rufo jikin ki ki dawo.
    Hakan nan ta tashi ta rufo jikin ta da pink bedsheet wanda tafiya take yana ja a qasa har ta qaraso ta zauna.

*```Billy giro😊```*

®NAW✍truncated by WhatsApp]
[9/22, 5:48 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [7/29/2016] Billy giro😊:

*```👛BILLY PINKY DURLING```*👛



*```Na```*

*```Billy giro😊```*

*```Page```*
     *```👛6 to 7👛```*
Abba ya kalli Hakeem yace "kudi nake buqata daga gurin ka, ka kawo iya qarfin ka.

Hakeem ya shiga lalubar aljihun sa, akwai kudi sosai amma yaji sunyi kadan da ya bawa Abba su.
   Nan ya kalli Abba yace"kayi haquri Abba ina zuwa"
    Tashi yayi ya tafi 6angaren sa ya dauko kudi bandur d'in dala dala sabbi dal har suna sheqi,ya kawo yace "gasu Abba"Abba Yace"mamana zaka ba"ba musu Hakeem ya miqa mata kudin yayinda shida ita suka shiga mamakin me Abba ke shirin yi.
   Billy ta kar6i kudin kenan Abba yace"sadakin ki ne!gaban ta ne yayi mugun faduwa har sae da kud'in suka sa6ule daga hannun ta,bcs duk a tunanin ta kiran da Abba yayi musu zai ce an fasa zancen had'a auren su, sae gashi taji zancen sadaki,nan taji gabadaya kamar bata tare da jikin ta domin ko qaramin yatsan ta ta kasa motsawa.

Hakeem kuwa takaici ne ya kawo masa iya wuya yana kallon Billy kamar wanda kejin ya shaqe wuyan ta ta mutu kowa ma ya huta.
  Ya kalli Abba ya kuma sake kallon Billy a wulaqnce tare da nuna ta da yatsa yace"Abba dama akan wannan abar ne ina da kud'i a aljihu na amma naje na d'auko en dala dala sabbi dal na kuma bata da hannu na a matsayin na bata sadakin ta,please Abba don Allah ku ajiye zancen auren nan wlh idan akayi shi akawai babbar matsala.... Hakeem! Idan muka had'a wannan auren kai ka dad'e baka kashe mamana ba! Inace iya babbar matsala kenan!
   Yana gama fadar haka ya kalli Billy yace "mamana dauki kudin ki tashi ki tafi Allah shiyi miki albarka domin a yau naji dad'in da baki ce komai ba, kuma zan neme ku anjima idan muka gama yanke shawara da Abbanki.
    Da qyar Billy ta Kai hannu ta d'auki kudin tana mai jin tamkar garwashi ne ta jimqa a hannun ta.
    Tafiya take kan staircase yayinda qwalla suka cika tap a idonta har ma bata ganin hanya sosai,sae roqon Allah take a cikin ranta Allah yasa ta mutu kafin ta kai d'aki ko zata huta da mummunan abun da ke shirin faruwa da ita.

Tana isa d'aki ta saki bedsheet hade da kudin da ke hannun ta,ta zauna kan bed tare da dafe kanta da taji yana mugun sara mata, ga kuma wani zafi da taji yana fita a jikin ta.


A main falo kuma,
 Billy na wuce wa,
 shima Abba ya tashi yace da umma"ni zan fita"tace a dawo lafiya"nan ita ma ta tashi.
   Suka bar Hakeem da yaji an sake lalata mishi tafiyar sa zuwa new Delhi, kan neman su da Abba yace zai yi anjima.

Billy dake d'aki taji zafin sae qaruwa yake nan ta tashi ta zuge zip din rigar ta hade da zare hannayen rigar sae kawai taji an bude qofa,tayi saurin dafe rigar ta dake qoqarin zamewa daga qirjin ta tare da kallon wanda ya shigo.

Wata kyakkyawar yarinya ce er 18yrs tsara ne da Billy da alama qawar ta ce.

Ta rufe qofa tare da fadin"pinky lafiyar ki nayi knocking kusan 3times naji shiru har na d'auka cewa kina bayi?
   Cikin muryar kuka Billy tace"ta ya zan jiki feenah bayan ina cikin babbar matsalar da ban ta6a haduwa da ita a rayuwa ba, ban kuma ta6a tunanin zan hadu  da ita ba.

Cike da damuwa feenah ta zauna tace"pinky wace irin matsala ce haka?hawaye masu zafi ne suka zubo a kumatun Billy tace"feenah aure za'a hada ni da wanda a duk duniyar nan ba wanda na tsana kamar shi, wanda na tsani ganin sa ko a mafarki.

Sosai damuwar Feenah ta qaru tace"waye shi? Kuka Billy ta fashe dashi tace"Feenah wa kika sani banda Bobby!wa kika san na tsana bayan shi!

Feenah ta lumshe ido hade da sauke ajiyar zuciya tace a ranta
_"ina ma ce nice za'a had'a aure na da Bobby yanda nake mutuwar son sa, oh Allah!meyasa ka bawa Billy wannan dama wacce kwata kwata bata da buqatar hakan"_

A hankali ta bude idon ta ta dafa Billy tace"wlh pinky kinyi babbar sa'a zaki zamo matar Bobby.... Ba shiri billy ta buge hannun ta taja  baya kamar wacce taga abin tsoro ta nuna Feenah da yatsa yayinda mamaki qarara ya bayyana a fuskar ta tace"Feenah ashe dama ba kya sona ban sani ba sae yau!

Idan haka ne pinky me kike son cewa da su Abba da ke qoqarin hada auren ku? Feenah su Abba sun yi haka ne sbd kiyayyar da muke yiwa juna nida Bobby tana matuqar damun su,shiyasa suke son hada auren mu domin kamar ganin suke hakan zai sa mu daina nuna wa junan mu qiyayya,, amma ke cewa fa kika yi wai nayi babbar sa'a zan zamo matar Bobby, haba Feenah! kina magana kamar wacce bata san abinda take yi ba.....nasan  abinda nake yi pinky, Bobby baya da matsala ta koina matsalar sa d'aya ita ce qiyayyar da yake nuna miki......U have gone mad! Feenah ko ba qiyayya me zanyi da wannan gardin mai qirar samudawa! kece ke ganin haka pinky, amma Hakeem kyakkyawa ne giant man wanda duk mace mai aji ta kalle shi sau d'aya zata so ya kasance mijinta, Bobby sam baya kama da samudawa shi dai kawai cikakken namiji ne wanda ya had'u ta koina baya da makusa...... Feenah!! Wlh idan har maganar bobby zaki tamin fitar min daga d'aki!
  Feenah tayi shiru tana kallon Billy da ta fita hayyacin ta a lokaci d'aya,
Sae ta sami kanta da qara jin ina ma ace ita ce zata auri Hakeem.

               *```°°°°°```*
Hakeem kuwa yana tashi ya nufi 6angaren sa ya hadu da Amjad yana qoqarin kiran sa a waya.
     Bai cema Amjad komai ba ya shige daki.
   Amjad ya bishi, yayi tsaye yana kallon Hakeem da yayi baqiqirin da rai"Yace haba Bobby sae ka ce nine na dora ma pink lips.....mtsw Amjad ba ma wannan ba, baka san matsalar da ke faruwa ba, wai ace ni su Abba zasu hada aure da wannan dabbar,
 kalar en yunwa wacce ko iskan qwarai ya busa zata iya karye wa, gata da fuska kamar ta aljannu..... Thank God!wlh naji dadi da Allah ya kar6i roqo na!domin na jima ina roqon Allah yasa su Abba su muku haka inga qarshen qiyayya......kukan kura Hakeem yayi ya cakumi kwalar Amjad ya nuna shi da yatsa yayinda idanuwan sa sukayi jajir jijiyoyin kansa duk suka tashi, yace"wato kai ne ka roqi Allah! to bari kaji wlh addu'ar ka bata kar6u ba idan ma har tunani kake ka daina, domin idan har dani za'a d'aura auren to za'a gani!nan ya iza Amjad waje ya kulle qofar dakin da qarfi ya kuma saka key, amjad ya tashi da murmushi ya kakka6e jikin sa ya tafi yana mai mamakin wannan qiyayyah tasu Hakeem wai kuma en uwan juna ne.

*```Billy giro😊```[truncated by WhatsApp]
[9/22, 5:52 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [7/31/2016]

*```👛BILLY PINKY DURLING```*👛


*```Na```*
   *```Billy giro😊```*


*```Page```*
       *```👛8-9👛```*
Da yamma Abban Billy ne da Abban Hakeem da kuma Billy zaune a main parlor suna jiran fitowar Hakeem.
   Abban Hakeem yace wai shi Hakeem ajiye mu yayi da zai bar mu muna zaman jiran shi.
  Abban Billy yace da billy"me yace da ke da kika je kiran shi? nifa Abba nayi ta knocking yaqi ya bud'e ni kuma nazo abu na"amma shine kika bar mu muna ta faman jiran shi,wata qil ma baya nan,kira mana shi a waya muji,,Abba nifa banda number shi,girgiza kanshi yayi yana mai kallon ta kafin yake bata numbar Hakeem ya kuma ce sae tayi saving kafin take kiran shi, *village man* shine abinda tasa ma numbar sannan tayi dialling.

Hakeem da ke d'akin shi yana kankanta komai na dakin kamàr su frames da pictures duk ya tattara su ya saka a wardrobe haka shoes da duk wani  abu da yake buqa ta ya zuba su ya rufe wardrobe sbd shi a bakin rai yake baza a daura auren da shi ba, da zarar yaje new Delhi sae wanda ya ganshi domin daga can zai cira wata qasa.

Yana cikin haka ne wayar shi ta shiga ruri har ya dauki wayar sae kuma ya jefar kan bed sbd baya receiving call d'in new number,wayar na gab da tsinkewa ya danyi guntun tsaki hade da daga wayar ba tare da yace komai ba.

Billy kuwa Hakeem na d'aga wayar,
 murya ciki ciki tace kazo Abba na kiran ka, daga haka ta kashe wayar bata jira jin shin yaji ko bai ji ba.


Ba 6ata lokaci kuwa sae ga Hakeem.
   Ya gaida su Abba ya nemi guri nesa da Billy ya zauna.

Abban Hakeem ne ya shiga magana inda yake cewa"kafin nace komai idan na fadi abinda ya tara mu anan,Hakeem da mamana bana son jin komai daga bakin ku har sae na baku damar hakan.

Zancen dai daya ne kan auren ku wanda mun gama yanke hukunci gobe da qarfe goma sha daya na safe za a d'aura aure!

Sunji zancen tamkar dirar mikiya,
 sae dae dole sukayi shiru,domin bin umarnin,sae dae kallo daya zakayi musu kasan ba qaramin tension suka shiga ba.
   Sosai Hakeem yaso yayi magana amma Abba bai bashi dama ba.

Abba ya fitar da invitations masu yawa dake hade guri daya cikin envelope ya bawa Hakeem yace"sae ka fara gayyatar abokan ka kafin gobe,,Hakeem ya kauda kansa domin ko invitations din baya son gani yace "don Allah Abba ina da magana,
idan kasan ta zancen auren ku ce kar ma kayi domin ba abinda zamu canza!

 Ba ita bace Abba,
 yau nake so na fara hanya zuwa new Delhi,,, ana zancen auren ku kake zancen new Delhi da ba komai zai kai ka ba in  banda hutu,, asibiti zanje Abba shine nake son na isa abuja a yau domin na bi jirgin safe, wane irin ciwo ne kake dauke da shi da baza ka jira har a daura aure ba?
shiru yayi domin idan ya fad'a a shirme Abba zai dauki abin ba kuma zai barshi yaje ba,can yace"Abba ina da matsala a jiki na ne wacce bana so nayi sati d'auke da ita,,,Hakeem wannan ba uzuri bane da zaka ce baza ka jira a daura aure da kai ba, asali ban ga alamar wani  ciwo a tare da kai ba da har zai kai ka new Delhi!
   Don haka ban baka umarnin kaje ko ina ba!
Can yayi shiru yana tunani irin nasu na manya yayinda ya tsure Hakeem da kallo yace"sae dae kuma kasancewar ban san me ke damunka ba wanda baka so ka fad'a, zan barka kaje amma har sai an d'aura aure, amma kasani tare zakaje da mamana!wani irin abu Hakeem yaji yayinda ya dago yana kallon Billy cike da takaici haka ita ma take masa mugun kallo,suna cikin kallon juna suka shiga magana da zukatan su,kamar haka:
  Hakeem yace
_"akanki bazan ta6a bijirewa mahaifina ba tabbas zan bi umarnin sa amma sae kinyi babbar nadamar bi na a new Delhi domin abin da zan miki zai sa ki gudu da qafafun ki kuma ko kinzo gida zan miki qazafin da idan su Abba suka ji baza su ta6a yarda su maida auren mu ba_

 Billy tace"
_Tabbas cike nake da baqinci na kasancewa matar ka,sae kuma na hadu  da wani baqin ciki wato na biyar ka zuwa new Delhi amma zan jure domin na fahimci wata dama ce ta same ni wacce  zan nemi hanyar ku6uta daga aurenka,ku6uta ta har abada, domin zaman da zanyi da kai a new Delhi  qalilan ne,na gudo tare da maka sharrin da idan su Abba sukaji baza su ta6a fatar na sake zama matar ka ba har abada!_

*```Billy giro ``[truncated by WhatsApp]
[9/22, 5:58 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [8/1/2016]

*👛BILLY PINKY DURLING👛*


*Na*
*Billy giro😊*


*Page*
 *👛10-11👛*
Nan Abba yace"kuna iya Ku tashi ku fice.
   Amma mamana ki jira kad'an yanzu naki invitations na kan hanya ki samu ki rabawa abokanan ki kafin safe.
   Nan Hakeem ya fice bai damu da daukar invitations din da Abba ya bashi ba.
   Billy kuwa ta d'ago kanta ta kalli Abbanta da shima ita yake kallo.
   Yace "zo mamana"
 cike da son tayi kuka ta tashi taje,ya kalli yanda hawaye ke qoqarin fitowa a idanun ta, yace"mamanah yanzu ashe ba muyi matsayin da zamu yanke hukunci akan ku kuyi haquri da shi ba sae kunyi ta sa damuwa a ranku,hawaye ne suka zubo mata yayinda take kallon Abbanta, ta kwanta kan jikin sa tare da fadin"kayi haquri ba haka bane amma Abba hukuncin da kuka yanke ne yayi tsauri.
  Abba bai ce mata komai ba sae lallashin ta da ya shiga yi.

    Sosai Abban Billy ya shiga damuwa yayinda yake ci gaba da lallashin ta sbd ko kadan baya son ganin ta cikin damuwa, amma kuma dole tayi haquri da hukunci su domin sun gaji da qiyayyar da suke yiwa juna ita da Hakeem.

Washe gari tun da safe umma ce ta shiga d'akin Billy da sallama ta same ta kwance duk tunanin duniya ya dame ta.
   Tace"Billy tashi kiyi wanka ki shirya ki sami abinda kika ci, sbd yanzu nan Abbanku ya gama waya da mutanen Maiduguri suna gab da isowa (cewa da familyn su dake zama a garin maiduguri)

kuma kar ki saka qananin kayan da kike sawa iya cinya,ki sami doguwar riga ki saka.
  Tana gama fadar haka ta fita,kafin take cewa kiyi sauri fa.

Nan Billy ta tashi da qyar ta fad'a toilet, ta jima sosai kafin take fitowa sbd haka take jimawa gurin wanka kamar wacce ke shirin canza fata.

Koda ta fito ta sami umma ta shigo dauke da wata leda, ta bude ledar duk turarukka ne a ciki masu qamshi domin kafin ta bude ledar ma kamshi har ya cika daki.
    Umma tace "kinga har sun iso ga turarukkan da na bada saqo da kuma wadan da suka zo miki da su, sae ki fara aiki da su tun yanzu.

Nan umma ta fitar da turarukka kusan kala goma,kuma kowanne da kusurwar da ake shafa shi.
  Da yake dama Billy ba kunyar umma take ji ba, nan umma ta shiga shafa mata turarukkan kowane lungu da saqo na jikinta, amma banda na qirji da kuma private part,
Billy taje toilet ta shafo ta dawo, wanda ita dai biye kawai take da umma,kuma dama ita ma'abociyar turare ce sosai wacce ko kusa da ita ka tsaya zaka iya kwasar qamshin turaren jikin ta ba tare da ka ko ta6a ta ba.

Umma bata bar dakin ba sae da ta shirya Billy tsaf ta kuma tsare ta sae da tasa ma cikin ta wani  abu.
    Sannan ne aka bawa en uwa da abokan arziqi damar shigowa.

Guraren 11 gidan kamar ya tsage sbd mutane sun cika maqil kyace an jima ana zancen auren.

Haka shima Hakeem a 6angaren sa duk cike yake da abokanan sa,wanda a bakin su ne yake jin amjad ne yakai  musu IV bcs Abba na ganin Hakeem yaqi daukar invitations ya kira Amjad ya bashi,haka ita ma Billy Feenah aka ba domin ansan Billy jibge su kawai zatayi.
 

Da aka daura aure ne abokanan Hakeem sae tsula masa tsiya suke suna barkwanci shidai jin su kawai yake, ko ba qiyayya me zai yi da Billy wacce ta riga ta bada kanta wa maza,gashi sam qirar Billy bata daya daga cikin tsarin matar da yake so ya aura acewar billy tayi mishi sililiya sosai,
 don haka bai ga abin tsinta a jikin ta ba.


Haka ita ma Billy abokanan ta keta mata tsiya yayinda wata er uwarsu ta Maiduguri ta tsare ta tana zana mata lalle ba don taso ba,acewar lalata mata jiki kawai za ayi sbd dama Billy bata son taga digon komai a fatar ta,
 ra'ayin ta kamar wata baturiya, bata son lalle ko kadan qyamar sa ma take ji,hakan yasa a rayuwar ta bata ta6a lalle ba sae yau.


Sae gashi yayi matuqar kyau har dai yanda take da hasken fata,duk wanda ya gani sae ya yaba lallen.


Kwana uku akayi ana bukukuwa, en uwa da abokan arziqi kowa yayi farin ciki da auren domin kallo d'aya zakayi wa ango da amarya kasan sunyi bala'in dacewa da juna,kowa naji da nashi kyau ba wanda zai nuna ma wani.
   Amma su a gurin su basu ga ta inda suka dace ba suna dai jin mutane na fad'a kawai,wanda har ma haushi abin ke basu.
    Haka aka qare bikin da murna yayinda Ango da amarya suke cike da baqin ciki.

Da dare umma ce tayi ma Billy packing din zuwa new Delhi ta saka mata abubuwan gyaran jiki sosai hade da turarukka inda take mata bayanin amfanin su d'aya bayan d'aya, Billy sae kallon umma take ba eem ba um um.


Washe gari har air pot en uwa da abokan arziqi suka raka su sae da jirgi ya tashi sannan suka fice cike da kewar juna.

Billy da Hakeem ba abinda suke tunani a cikin jirgi face sharrin da zasu qullawa juna domin ku6uta daga auren.


Har suka isa ba wanda ya kalli wani  bare zancen magana,idan baka sansu ba baza ma kace sun san juna ba.

Da yake dama new Delhi gurin zuwan su ne, wato sun saba zuwa dasu umma.
    Jirgin su na sauka kowa ya kira drivan shi yazo ya d'auke shi.

Masaukin su d'aya ne amma yau kwanan su biyu ba wanda yasa wani a ido, wanda hakan yayi ma Billy dadi sosai har ma tana roqon Allah yasa wani  masauki Hakeem ya nema.


Kusan kullum sai ta fito tana zagayawa a cikin gidan sae yau taji bari ta shiga room by room.

Sanye take da er riga mai hade da wando iya cinya rigar handless ce dai dai ita,gashin kanta a sake yake sae cat eye sunglasses da tayi qawa dashi  saman kanta,riqe take da glass cup mai dauke da fresh milk a ciki,
 da yake dama ma'bociyar shan ta ce.
  Haka take tafiyar ta cike da natsuwa har taje room d'in da daga shi sae d'akin ta.
   Tana bude dakin ta shiga dai dai Hakeem ya fito daga wanka, ba shiri ta kauda idon ta,ta juya cikin sauri zata bar dakin,Hakeem ya jawo ta da qarfin tsiya ya manna ta a jikin gina,sae duk fresh milk din da ke hannun ta ta watso masa a qirji, wanda yayi dai dai da faduwar eyeglass din da ke saman kanta,kar6e cup din yayi, ya kama hannyen ta duka biyu da da'yan hannun sa, ya mayar a baya ya jimqe gam,har yana qoqarin jefar da glass cup sae kuma ya fasa, ya kalli Billy wacce ta kauda kai ta rumtse idonta gam, ta qara qanqame jikin ta da jikin gina bata son ta ta6a jikin Hakeem da yayi mata rumfa, qirjin ta sae kai komo yake, har ana jin sautin fitar numfashin ta sauri sauri sbd ta tsora ta sosai da ganin Hakeem ba komai a jikin sa,bcs bata ta6a ganin namiji haka ba sae yau ko lokacin da ta ganshi da jennifer bata ga tsiraicin sa ba sbd Jennifer ta masa rumfa.

Bai damu da ta tsora ta ba,
 sae ma wata uwar tsawa da ya daga mata yace"uban me kika zo yi a daki na kuma dai dai lokacin da nake fitowa daga wanka!?bud'e idon ki kiga yanda kika 6ata min jiki!ki bud'e idon ki nace!!cike da tsiwa Billy ta bude idon ta ta tsayyadda duban ta a iya qirjin sa, ta buga uban tsaki ta kauda kai,sae mutsu mutsun qwatar hannun ta take,tace "dallah malam ka sake min hannu na fita!ran Hakeem ne yayi mugun 6aci yace"ba inda zaki je sae kin lashe kaf abun da kika watsa min a qirji, ko kuma wlh na tu6e ki na shafa miki ita a naki qirjin!

*```Billy giro😊```*

®NWA✍truncated by WhatsApp]
[9/22, 6:02 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [8/2/2016] Billy giro😊:
 *👛 BILLY PINKY DURLING👛*


*Na*
*Billy giro😊*

*Page*
    *👛12👛*
A wulaqance Billy ta kalle shi sama da qasa tace"u have gone mad!
  dallah ni ka sake min hannu na wuce ko kuma wlh duk abin da na maka kai kaja!

Da mamaki Hakeem ke kallonta ya rasa me yasa Billy ta raina shi da yawa,amma yau zai yi maganin ranin domin sae ya tu6e ta kaf ba zai barta da komai na jikin ta ba.
   Nan yakai hannun yaja rigar ta da qarfi har sae da rigar tayi qara.
  Cike da masifa cikin daga murya Billy tace wlh kar ka yaga min riga! Hakeem bai saurare ta ba sae qoqarin yaga rigar yake ta qarfin tsiya, nan Billy ta rikice ganin da gaske yake, gashi tayi iya qoqarin ta na ganin ta qwace kanta amma ta kasa.

Inda Allah ya taimake ta high heel ta saka, bata tsaya wata wata ba ta daka masa tsinin takalmin a qafa ta kuma fizge kanta da qarfi ta ture shi ya fada kan bed yayi saurin jawo bedsheet ya rufe jikin sa.

Ita kuwa Billy tayi saurin zare makullin qofa ta fita da shi, ta rufe Hakeem ta waje tana jin sa yana dukan qofa yana fadin"kizo ki bude min qofa ko kuma duk na fito ki gane kuren ki!
  Nan ta gudu ta bar key a jikin qofa.
   Tana shiga daki ta fada ruf da ciki kan bed tana sauke numfashi.

   Bata yarda ta fito daga dakin ba sae da safe.

 Ta fito sanye da doguwar rigar er simple amma ta mata kyau sosai sbd Billy mace ce wacce komai munin sutura idan ta saka suna mata kyau.

   Ko wannan karon riqe take da fresh milk, yayinda take
saukowa  kan staircase ta hango Hakeem zaune a falo yana waya rai 6ace ya dora qafa kan centre table qafar ta qabe sul sae sheqi ta ke.
     Yana hada ido da ita ya sakar mata mugun kallo.
   Duk da ta tsorata haka ta dake tabi ta gaban shi ta wuce zuwa garden.
   Inda ta zauna kan resting chair tana kur6a fresh milk a hankali cikin natsuwa.


Hakeem kuwa ya matsu bai gama wayar da yake ba yazo ya sami Billy.


Tana tsaka da hutawar ta sae ga Hakeem cikin yanayin 6acin rai wanda bata ta6a ganin sa ba kamar wanda allurar sa ta soja ta motsa,shiyasa ta tsorata sosai amma bata yarda ya fahimci hakan ba sae ma kauda fuskar ta tayi gefe tana ci gaba da shan fresh milk.

Bata ankara ba taji ya kar6e kofin ya jefar da shi, ya damqi gashin kanta tare da dora qafar sa kan qafar ta yana mutsutsuka qafar,wani  zafin bala'i taji wanda yasa ta shiga yin ihu yayinda Hakeem ke fadin"wa ya sanar dake abinda nazo yi garin nan da har zaki sanar da Abba, wanda dalilin haka ya hana min na aikata abin da nazo yi,ki gaya min munafurci me yasa kika sanar da Abba!

 Billy kam bata iya ce mishi komai ba sae qoqarin qwatar gashin ta take, kuma bata ma fahimci zancen da yake ba, gashi kuwa ya zage sae fad'a yake, yayinda yake ci gaba da mutstsukar qafar ta,ita kuwa tana faman ihu,
    Wayar sa ce tayi qara ya jefar da Billy ta fada sae kan resting chair ta riqe qafar ta da tayi jajir,Hakeem kuwa ya fita tare da rufe Billy a cikin garden.

Nan Billy ta shiga kuka domin ta fahimci hadarin da ya gani ne yasa ya mata qeta.


Ba 6ata lokaci ruwa suka fara sauka sosai, Hakeem kuwa yana jin yanda ruwan ke sauka da qarfi amma yayi kamar ya manta da Billy da ya rufe a garden, da qarshe ma baccin sa yayi.


Yana cikin bacci ne wayar sa ta tashe shi, koda ya duba yaga Amjad, ya d'aga wayar hade da tsaki yace"Amjad meye haka ina bacci ka tashe ni,dariya Amjad yayi yace"kaga malam inace an fasa zancen canza pink lips ba....mtsw bari kawai Amjad ashe er iskar yarinyar can ta sanar da Abba shine yau har nayi shirin zuwa asibiti ya kirani ya hana min,har yana rantsuwa akan idan nayi nida shine...kai kar ka zargi Billy fa bata ma san da zancen ba wlh nine na sanar da Abba domin na fahimci baka da hankali,,amma Amjad....nan Amjad ya kashe waya, ran Hakeem yayi mugun 6aci,sae zagaye dakin yake kan taikacin amjad, can yaje ya bud'e Billy da ke garden ya koma falo ya zauna rai 6ace yana ji kamar yayi tsuntuwa domin yaje su yita shi da Amjad.


Cike da damuwa ya jingina a jikin sofa tare da lumshe ido, shigowar Billy ce tasa ya bude idon shi a hankali yana kallon yanda ta jiqe sharkaf kuma da qyar take taka qafar ta.


Saurin jaye idon shi yayi,sbd rigar jikinta ta manne sosai har tana qoqarin bayyana sirrin jikin ta
domin d'an kallon da ya mata har ya fahimci cewa"duk da kasancewar ta sililiya tana da boobs da hips da kuma baya d'an dai dai.


Billy kuwa na shiga daki ta cire rigar jikin ta, ta zamo daga ita sae pant sbd dama ba Bz a jikin ta sbd boobs d'in ta basa buqatar bz.
  Kwantawa tayi kan bed ta rufe jikin ta da bedsheets sae rawar dari take,nan take zazza6i mai qarfi ya debe ta.



*Billy girotruncated by WhatsApp]
[9/22, 6:05 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [ 8/3/2016] Billy giro😊:
*```👛BILLY PINKY DURLING```*👛


*Na*

*Billy giro😊*
*page*
     *👛13👛*
 Har dare Billy na fama da zazza6i Hakeem kuwa baya ko gidan,kuma da ya dawo bai bi ta kanta ba duk da yasan idan ruwa suka dake ta zazza6in qwarai take domin wani lokaci har kwanciya sae tayi a asibiti.
  Bashi ya fito ba sae da safe domin motsa jiki,tunda ya fito balcony ya fara jogging a hankali har yana gab da fita gidan se wayar sa tayi qara.
  Koda ya duba yaga Abba, nan ya shiga tunanin yau kuma wane irin fada zai sha.
  Yana daga wayar kuwa Abba ya shiga yi masa fada sosai sae da ran Hakeem yayi baqiqirin.
  Hakeem bai fita daga gidan ba ya koma daga ciki inda ya zarce sae dakin Billy.
   Yana bude dakin qamshi ya daki hancin  shi,
 yayi tsaye na en sakwanni kafin yake 6allah wutar dakin.
   Ya hango ta rufe shif da bargo kanta kadai ake gani.
   Yayi kiran ke! ke!tayi banxa dashi kuma idon ta biyu, Hakeem da wayar sa ke  hannun sa yace"kaji ko Abba tana ji na fa ta share ni,"bana son shashanci ka kira sunnan ta ne bare ta share ka, oya kira sunan ta,,,Hakeem da ko kadan baya son furta sunan Billy a bakin sa yace"ai bacci take a bari idan ta farka zan kiro mata doctor ya duba ta,...yanzu dai nake son ka taimaka mata ta shi ka kuma bata wani  abu tasha kafin ka kirawo doctor,ba yanda Hakeem ya iya domin vedio call ne, Abba na ganin duk abin da yake.
  Ajiye wayar yayi saitin inda Abba ke hango shi, yaje yayi tsaye yana kallon ta,
 ya rasa ma ta yanda zai tashe ta.

Billy kuwa bata ko san Hakeem ya ta6e ta bare zancen ya taimaka mata ta tashi, dole ta yunqura da qyar ta tashi,
 shi kuma Hakeem yaje ya duba fridge din dakin ya dauko fresh milk,Abba yace"a'a Hakeem abu mai zafi zaka bata, ba yanda ya iya dole yaje dakin sa ya hado mata tea domin bai ga alamar kayan tea a dakin ta ba
   Yana bawa Billy ta saki cup ya sa6ule sae qasa,wanda tayi haka ne da gangan sbd bata jin zata iya shan abinda ya fito daga hannun Hakeem.

 Hakeem yayi saurin jaye qafar shi kar tean ya watso masa, sae da ya kalle ta kafin yake kallon wayar shi yace"ka ganta ko Abba... Haba Hakeem ina taga qarfin riqe cup wacce ke fama da zazza6i mai qarfi haka.
Sagarci ne kawai Abba...ba wani  meyasa da ana ruwa baka hana ta shiga ruwan ba bayan kasan bata shiga ruwa,nan Hakeem ya kalli Billy da yaji ashe bata fad'i ainihin yanda abin ya faru ba, yace"Abba garin baqin yawon ta ne da take zuwa duk dare daga can ruwa suka tare ta"Billy ta kalli Hakeem wanda ya furta a ransa cewa"
_indai sharrri ne yanzu na fara miki kafin na kai ga babban_
 Billy kuwa tace"
_indai sharrin ne sae dae muyi wa junan mu_
  Abba yace"mamana kina matar aure kike fita yawon dare"cike da shagwa6a har tana fitar da qwallah a idon ta tace"Abba shine kullum yake fita yawon zuwa club ya barni ni kad'ai a gida ina ta faman jin tsoro dole sae na fita neman shi...ke!,,qarya na fada ka rantse idan baka zuwa club duk  dare, ganin yayi ta ma raina shi idan ya rantse dole yayi shiru Abba nata zabga mishi fada, da qarshe yace maza ka tashi ka hado mata wani  tean kuma idan ka hado kai zaka bata da kan ka,nan Hakeem yaji duk duniya Abba ya zubar mai da class.
  Bai tashi ba sae mugun kallo da yake ma Billy har Abba yakai  ga daka mishi tsawa sannan ya tashi ya hado wani  tean ya dawo,ya zauna kan drawer da ke kusa da gadon,ya dora cup a bakin ta wanda cikin qeta ya karkata cup don kawai tean ya shiga da yawa ya sarqe ta, Billy da bata ma bude bakin ta ba tean ya kwarara sae cikin jikin ta,wani irin kafirin sanyi taji kamar ruwan qanqara,nan ta buga ihu sosai tana fadin wayyo Abba ya qona ni mugun zafi ne da tean, a rikice Abba yace"haba Hakeem yi maza ka duba ta, Abba na duba ta sae kace wani  doctor, kuma a qirjin ta ne fa, bana son shashanci kai ba mijin ta bane, zan kashe wayar na baka minti biyu ka duba ta.
  Nan Abba ya katse wayar.
  Hakeem yace"oya sae ki bude qirjin naga inda kika qone, yayi maganar ne cike da fuskewa bayan ya duk san cewa da ruwan qanqara  ya had'a tean.
  Billy tace"ce maka akayi ni irin Jennifer ce da zan bude jiki na ka kalla....wlh kar ki sake kawo min maganar wannan er iskar, kuma duk kika sake min sharrin zuwa club se kinyi nadama....mtsw bayan ka lalata yarinya ka gama da ita shine kake kiran ta er iska, sannan kuma ko ynzu ka sake min sharri gurin Abba zan maka wanda ya fishi,ai sa'a ma kaci bance a buge kake dawo wa gida ba....kodai ke kikayi sa'a bance  gurin wani  gardi kike zuwa ba,da tun gida Abba yasan aikin ki ne, tara gardawa a main parlour kuna sheqe ayar ku, shine aka wani  laqa min ke don kar wani  ya aura ya fahimci abinda ke nan.
    Yana gama fad'a ya buga tsaki ya dauki wayar shi ya cire battery don kar Abba ya sake kiran shi,sannan ya fita daga dakin.


*Billy gir[truncated by WhatsApp]
[9/22, 6:06 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [8/3/2016] Billy giro😊:
*👛BILLY PINKY DURLING👛*


 *Na*
*Billy giro😊*

*👛14👛*
 Tsaki kawai Billy tayi ta kwanta,ita tasan kanta ba zata ta6a damuwa don wani  ya dauke ta a er iska ba, shida ma ta kama dumu dumu har yake jin qarfin kira mata er iska.

   3 days letter

Yau kusan kwana uku Hakeem bai sa Billy a ido ba amma hankalin sa a kwance sae harkar gaban sa yake.


Billy kuwa zazza6i ne ya hana ta fitowa sae yau ta d'an ji qarfin fitowa parlour ta kwanta.

Hakeem ne ya fito ya same ta a kwance tana waya.

  Gashi ya fito ne domin sauraren labarai kuma baya jin zai iya hada gurin zama d'aya da ita,ma'ana gabadaya baya son ganin ta a parlourn, nan yaje yayi tsaye a kanta Yace"kinga malama ki tashi ki bani guri zan kalli labarai! Billy kam gyara kwanciyar ta ma tayi taci gaba da wayar ta.
  Yace"da ke nake magana kina jina fa! nan ta tashi hade da tsaki tace"sorry durling wlh wani crazy dog nake fama da shi kullum ya ganni sae ya dame ni da haushi,,uhm to ya na iya an kawo min shi ya riqa min gadi,ta fadi haka ne yayinda waya ke maqale a kunnen ta zata hau upstairs.
    Ran Hakeem ya 6aci da jin ta kira shi crazy dog, nan ya fizge wayar da ke hannun ta ya jefar,wanda yayi dai dai da fadowar Billy kan jikin sa sbd wani  irin jiri ne ya debe ta, duk tabi ta qanqame Hakeem sbd yanda gidan ke juya mata.

Har hakeem yayi
niyar sakin ta ta fadi sae ya fasa sbd yanda yaji jikin ta da zafi sosai, ta kuma dafe goshin ta,kauda kan sa yayi yana mai sauraren muryar da ke fitowa a cikin wayar Billy da ya jefar, muryar wata frnd din ta ce sae faman kiran"pinky durling what happen!hope is not crazy dog hot u!pls pinky say something.

   Hakeem ya kauda kansa ya kalli Billy da ke jikin sa wacce har yanzu jiri bai sake ta ba,bai damu da hakan ba yace"kinga malama sae ki tashi kan jikin Hakeem kike ba wani  gardin da kika saba kwañciya a jikiñ sa ba! Duk da abinda Billy keji bai hana tace"mtsw ai da kaga zan fadi da ka bar ni na fadin"tana gama fada ta wuce bata bi ta kan wayar ta ba.

Da dare Hakeem ne sanye da farar singlet da farin wando three quarter, yana riqe da laptop da kuma wayar Billy.

Dakin Billy ya shiga ya same ta gaban mirror daure da towel tana shafa turarukka.
    Tace "meye haka zaka shigo min daki ba sallama ba knocking,bai ce da ita komai ba sae dae fuskar nan tashi a daure yace "kar6i umma zata yi magana da ke.
   ta kar6i laptop din yayinda Hakeem ya fita,ta dora laptop kan mirror cike da murna tana kallon umma da ita ma billy take kallo, bayan sun gama gaisawa ne, umma ke cewa"wai har yanzu fadan naku na nan baku daina ba,a shagwa6e Billy tace "umma shine fa ya shigo min daki ba sallama ba knocking,oh ni! na rasa me ke damun hakeem da tun yana yaro yake fama da baqin rai har yanzu,,nan Billy ta basar da zancen Hakeem taja ta da wata fira, yayinda suke firar cike da nishad'i.


Hakeem ya jima sosai kafin yake dawowa.

shigowar sa keda wuya ya jefa mata wayar ta kan bed ya kar6i laptop din shi, rai 6ace Billy ke kallon wayar ta da screen ya tsage,cikin muryar kuka domin tana bala'in son wayar tace"amma Bobby sae yau na qara tabbatar da cewa kai bagidaje ne wlh!wato dazun fasa min waya kayi!
     Wani  kallo Hakeem ya mata na daban domin yau komai a daban yake yinsa cikin daure fuska sosai,yace"mind ur tongue!...naqi din!stupid village man!,,zanyi maganin abun....kayi man in zaka iya! juya wa kawai yayi zai bar dakin tace"Allah wadaran baqauyen mutum duk kabi ka farfasa min waya....rufe bakin ta keda wuya taji ya jimqo gashin kanta gam yaja da qarfi kamar wanda ke qoqarin cire mata sumar, yace"lallai yau zanyi maganin d'an iskan bakin nan naki...sosai billy ta tsorata da ganin yanda jikin sa ke rawa kan 6acin rai da alama akwai inda aka ta6o shi kafin ita,amma ta dake tace"kayi mana wa ya hana ka!
   Ai ko kamar jira yake ya jefa ta kan bed yayinda ya fada kan jikin ta ya daddanne ta ko motsin kirki ta kasa,a rikice take kallon yanda ya hau kan jikin ta duk tabi ta rude hankalin ta ya tashi sosai, bata qara shiga tension ba sae da taji ya hade bakin ta da nashi, yana tsutsar lips din ta cike da mugun ta, wanda jin zafin abun take tun daga tsakkiyar kanta har zuwa tafin qafar ta.
    Nan tayi ta yunqurin qwatar kanta amma ta kasa sae kuka da ta ajiye mishi.
   Sautin kukan ta ne ya qaru sbd Hakeem kamar ya fita hayyacin sa sbd yanda yake gudanar da al'amrin har yana hadawa da romance.
   Wanda da qyar ya dakatar da kanshi ya tsaya kallon lips din ta da sukayi jajir,ya dago idanun sa da suka canza kala ya kalli idon billy da hawaye keta faman sintiri,sae kallon qirjin ta  take, bai yarda ya kai idon sa ba, sbd yanda yaji hannun sa jimqe da wani  abu very soft duk ya cika masa hannu, saurin sakin abun yayi ya tashi cike da tsananin mamakin ya ma akayi shida zai punishing din ta a iya bakin ta, amma hannun sa yakai  kan qirjin ta.
   Nan ya fita da taikicin kansa da har yake biye wa Billy kan komai tayi yace sae yayi punishing din ta gashi yanzu ya qara ja ma kansa raini a banza!


*Billy girotruncated by WhatsApp]
[9/22, 6:13 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [ 8/5/2016] Billy giro😊: *👛BILLY PINKY DURLING👛*




*Na*

*Billy giro😊*

*page*
    *👛15👛*
Yana shiga daki ya zauna kan bed tare da dafe kanshi idanun sa duk sukayi jajir sbd haushin kansa da yake ji, da kuma wani  irin abu da yake ji na daban a jikin sa.
   Da qyar ya samu ya saisaita kansa,ya cire kayan jikin sa ya fada wanka sbd qamshin turaren Billy da yake jin ya cika masa hanci.
   Ya jima kafin yake fitowa sai yaji kuma dakin duk ya kwashi qamshin turaren Billy, guntun tsaki ya buga ya dauki kayan sa da ya cire ya saka a washing machine,sannan yabi dakin ya feshe da wani  turare sbd ya daina jin qamshin.


Billy kuwa tunda Hakeem ya barta ko qwaqqwaran motsi ba ta yi ba sai hawaye da ke ci gaba da kwaranya a idon ta,da qarshe ta fashe da kuka mai cin rai domin ganin take Hakeem ya gama da ita tunda har ya had'a bakin sa da nata ya kuma dora da lalabe mata jiki.
   Da qyar ta tsayar da kukan da take,
 ta tashi ta doro arwala ta saka tufafi sannan tayi sallar shafa'i da wuturi,kafin take gyara gadon ta da ya yamutse sannan ta kwanta.




Washe gari guraren qarfe goma ta tashi daga baccin safe,wani  irin radadi lips dinta ke mata kamar yanzu abun ya faru,
 jikin mirror taje tana kallon lips dinta da sukayi jajir,
 long time tana kallon abu daya,
 kafin take furta"I will start my plan from to day inshaAllah!
cikin takaici ta share hawayen da suka zubo mata.

 Sannan ta fada toilet tayi wanka ta fito ta shafe jikin ta da mayukka masu qamshi,hade da shafa turrukkan ta masu taushin qamshi.

Duguwar riga ta saka English wears mai dan siririn hannu rigar har qasa take amma gefe daya a tsage yake tun daga kan cinyar ta har qasa.
     Breast curve ne da rigar inda ta kama qirjin ta sosai tayi mata cak kamar a jikin ta aka dinka ta.
    gashin kanta a sake yake har baya yasha gyara sae sheqi yake, fuskar ta  kuwa er simple make up ce yayinda take sanye da fancy sunglass wanda ya qara bayyanar da karan hancin ta,qafafunta kuwa wasu takalma ne masu tsini kamar wacce zata je fashion.

   Wata er jaka ta dauko ta zaro orbit chewing gum ta saka a bakin ta.
   Ta kalli kanta a jikin mirror yayinda ta dauko fashion ear-ring ta saka se tauna chewing gum take cike da natsuwa,
 shu'umin murmushi tayi tare da fadin that's my plan but pinky u have to be patient what ever u see bcs its the beginning.


Fitowa tayi tana tafiya a wayance ba haniya sae daukar hankali.

Hakeem dake zaune a falo yana karatun jarida inda ya dora qafa kan qafa ya jingina a jikin sofa,fuskar sa ba alamar annuri bcs yana riqe da jarida ne kawai amma sae tuna abinda ya faru jiya yake,ba abinda yake tunawa ya qara jin takaicin kansa irin  hannun sa da ya samu dumu 2 jimqe da dukiyar fulanin Billy.

 Qamshin turaren Billy ne ya riski hanncin shi,inda  tazo gab da shi ta kai hannu ta dauki key din da ke ajiye kusa da shi bai ce da ita komai ba sae daure fuskar sa da qara yi,yana mai  kallon hannun ta da ta dauki makullin motar sa, kauda kansa yayi yaci gaba da karatun jaridar sa amma kuma ya d'an shiga mamakin Billy da ta dauki makullin motar sa abinda bata ta6a yi ba tun suna yara,domin ko kayan sa naja ga qasa baza ta6a sa hannu ta dauka ba,nan dai ya basar da zancen ya tashi ya bar falon.


Haka ta fita abinta ba wani  mayafi.
  Taje ta shiga mota tana fita gate din gidan ta sami guri ta parker mota ta bude jakar da ta ajiye a dayan seat ta zaro black After dress ta saka ta cire madubin ido ta dauki dan top tayi niqab dashi kamar wata balarabiya.
   Ta fitar da chewing gum din da ke bakin ta ta jefar sannan ta kalli kanta a jikin mirror tayi second biyar tana kallon kanta a cikin wasu kalolin tufafin da bata ta6a sawa ba se yau tace"thank u Feenah that u make my plan easy".
   Tana gama fadar haka taja motar,
 ta tafi shopping complex ta siyo komai da zasu buqata na abinci daga can ta wuce kasuwa ta kwaso sauran abubuwa hade da vegetables.


Da ta dawo bata yarda ta shiga gidan ba sae da ta cire After dress ta mayar cikin jaka hade da top,ta zaro chewing gum ta saka a bakin ta.

    Ta kuma maida madubin ido ta dawo kamar yadda ta fita.


Tana shiga gidan ta fito cikin mota a yangace ta jingina a jikin mota tana jiran mai gadi da ke ta faman sauri ya qaraso gurin ta.

cikin harshen turanci tace ya kira kuku ya kwashi kayan da ke cikin booth a shigar da su cikin gida.

Nan ta miqa masa makullin mota ta wuce.


Da shigarta ta hadu  da Hakeem ya na saukowa ita kuma tana haurawa,ba wanda yayi wa wani  kallon kirki duk da sun gogi jikin juna garin wucewa.

A gajiye ta shiga d'aki
ta cire kayan jikin ta ta fada wanka.

Hakeem kuwa fita yayi harabar gidan yayi zaune kan resting chair yana waya sae hango kuku yake wanda keta faman jidar kayan abinci yana shigar da su.
     ya d'an yi mamaki cos yasan Billy bata cin abinci sae can ba a rasa ba,
 iya karta,farfesu, drinks da fruits ko kuma tea,quaker oats da sauran su,abu me nauyi ne bata sa ma cikin ta.
 

Kuku na gama jidar kayan ya kawo ma Hakeem makullin mota,
wani banzan kallo Hakeem ya masa yace"am i d one that give it to u!?
no, sorry sir.


Nan ya kai ma gate man shi kuma yaje ya
 kaima Billy wacce har ta fito daga gurin wanka sanye da wata riga handless tsayin ta iya guiwa tana tufke gashin kanta da reborn sannan ta wuce kitchen ta had'a lafiyayyen abinci da tasan Hakeem na mutuwar so duk gida ya cika da qamshi.
 

Hakeem na shigowa gidan qamshi ya daki hancin sa hakan yasa ya kalli gefen dining inda ya hango Billy na jera kalolin abinci,Billy ta sake masa lallausan murmushi tare "da fad'in ur food is ready"
     Banbarakwai Hakeem yaji zancen wani  iri da kuma murmushin da yaga tayi, ya jima tsaye yana mamaki can ya girgiza kan sa cike da tsanar Billy yace a ransa
_"I got this drama,that's d problem,matsalar kenan na sosa mata inda ke mata qaiqayi shine har da wani had'a min girki just bcs ta sake samun dama ta, mtsw it was  a mad idea domin baza ki ta6a samun hakan ba_

Duk maganar da yayi bai san cewa maganar ta fito ba har ta sami isa kunnen Billy.
    Taji zafi sosai kan wata fahimta da yayi mata wanda yasa ta tuna abinda ya faru tsakanin ta da shi, har ta sami kanta da jin cikowar qwallah a idon ta,tayi saurin  hana zubowar hawayen sbd abinda taji zuciyar ta na fadi"be patient Pinky,just continue ur plan u will win inshaAllah.


Am sorry pls naso na muku da yawa domin har nayi nisa da typing din Page 16 but ban qarasa ba cajin waya ta yayi low amma by tomorrow morning inshaAllah zan muku posting.

*Billy girotruncated by WhatsApp]
[9/22, 6:21 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [8/6/2016] Billy giro😊:
 *👛BILLY PINKY DURLING👛*


*Na Billy giro😊*

*page*
 *👛16 & 17👛*
Nan ta wuce zuwa daki ta dauko hollandia milk tana sha cike da tunanin anya zata yi nasara akan plan din ta da ta fara kuwa.
 


Hakeem kuma yana shiga daki  ya kira kuku a cewar ya dafo masa indomie ba 6ata lokaci ya had'o mishi ya kawo.


Billy bata fito ba sae da qarfe hudu domin dorawa Hakeem abincin dare.

Bata yi mamakin ganin bai ta6a abinci da ta masa na rana ba sbd tasan da kamar wuya yaci.


Kuku ta kira ya kwashe kwanikan abincin taje ta sake hada wani  abinci sae dae abu mai sauqi tayi amma favourite din Hakeem,wato farfesun en ciki,sannan ta tuqa mishi founded yam da miyar  stew wacce aka sakawa ganyen alanyahu d'an dai dai ta kuma ji busasshen kifi, miyar sae qamshi take domin taji komai yanda ya kamata.
 

Cikin hadaddin kuloli ta saka abincin takai ta jera kan dining.




Daki ta koma tayi sallar magrib ta shiga toilet ta watsa ruwa, ta shirya cikin wasu kaya riga da wando English wears pink colour wandon ya kama jikin ta sae dae baya nuna tsiraicinta  tsayin sa  iya qauri, rigar kuma yanayin ta kamar vest din maza  amma ta mata kyau sosai sbd yanda ta kama jikin ta.


Koda ta gama shiri anyi isha'i,nan ta zuba hijabin ta tayi sallah.

Bayan ta gama ta cire hijabi ta linke ta mayar a wardrobe sannan  taje downstairs ta bude fridge ta dauko drinks din da Hakeem ke sha ta jera su kan dining.

Kai tsaye ta nufi dakin Hakeem ta danna door bell.
  Sae can Hakeem ya bude dakin.
   Billy ta d'an saki fuskar ta ba yabo ba fallasa tace ur dinner is ready.
   Daga nan bata ji me zai ce ba ta wuce ta bar shi nan tsaye da qamshin turaren ta a gurin tamkar tana tsaye.
  Tsaki Hakeem ya buga domin ganin yake bata da cikakke.
   Nan ya koma daga ciki ya jawo abincin da kuku ya dafa masa ya fara ci.



Billy kuwa dining taje taci farfesun en ciki ta tashi.

 Tana komawa daki ta dauki waya ta kira umma se firar su suke cike da nishadi.


Guraren qarfe goma ta sake wani  shirin kwanciya tazo downstairs ta kira kuku ya kwashe kwanikan abincin da Hakeem bai ko fito yaga tsarin sa ba.


Da safe kuma ta sake had'a mishi lafiyayyen break fast duk gidan ya cika da qamshi wanda sae maqiyin Allah zai ji qamshin abincin yace bai shiga ransa ba.
   Amma haka Hakeem ya bar gidan ba tare da ya kalli ko gefen dining ba.


Haka Billy tayi tayi masa girke girke kala kala ba tare da ta nuna gajiyawar ta ba.
   Wanda yau kusan wata daya tana faman yi ma Hakeem abinci amma bai ta6a zuwa ko kusa da dining ba bare zancen yaci,ko kadan hakan bai dame ta ba bcs sea tayi yunqurin saka damuwa a ranta wani 6angaren zuciyar ta ke hanata,yanzu ta kasance har dakin Hakeem take zuwa ta gyara idan ya fita koda zai dawo ta gyara masa dakin sa tsaf sae qamshi yake, gashi duk zai fita baya barin dakin sa da datti amma duk ya dawo sae ya fahimci an qara gyara dakin,komai bai ce mata sae kallon ta yake a wahalalliya mara aikin yi.


Haka ko fitar da takeyi ido ne kawai nashi ba ruwan shi da qananan kayan da take sawa ko oho,
 sae dae har yanzu idan ta fita sae ta sanya After dress  take shiga cikin gari.

   Wani  lokacin ma bata ko jin fita amma ganin Hakeem zaune a falo zai sa ta qirqiro fita ta kuma sa qananin kayan da ta san ko maqiyin ta yaga zata fita da kayan ba zai barta ta fita da su ba sbd girman zunubin da zata kwasa a matsayin ta na musulma kuma matar aure.
   Amma Hakeem ko a skin ba zai ce da ita komai ba, ba wai don yasan tana saka After dress a waje ba, sae don yanzu ma wani  takaicin ta yake qara ji domin ganin yake duk abubuwan da take tana yi ne,don ta karkato da hankalin sa ya sake sosa mata inda ke mata qaiqayi.
 
Wannan kenan

Kwance take tana sanye da er fincikar rigar ta ta bacci tana tunanin har yanzu plan dinta bai fara aiki akan Hakeem ba,ko dai zata canja wani  ne.
   Nan ta katse tunanin da kallon agogon dakin taga qarfe goma wato ya kama ta taje tasa a kwashe kwanikan abinci kar abincin ya kwana ya lalace

Hakeem kuwa tun 8:30 pm da ya dawo daga gurin sallah ya samu Billy ta gyara dakin very need, zanin gadon ya tanke sosai, wanda kallo d'aya Hakeem ya masa ya sami kansa da kwanciya kan gadon daga nan bacci mai nauyi ya dauke shi, sae can yunwa ta tashe shi koda ya tashi yaga har goma tayi kusa,
 a gaggauce ya shiga toilet ya watsa ruwa, ya dauko wayar sa domin kiran kuku,sae ya tuna cewa baya nan yayi tafiya,
 nan ya shiga tunanin ya zaiyi da yunwar da yake matuqar ji wacce sae abinci mai nauyi zai mishi maganin ta gashi komai bai iya dafawa ba,sae dai idan yau ne zai gwada hakan.

 Fitowa yayi domin zuwa kitchen kan ya qarasa ya hango abincin da Billy ta jera masa kan dining.
   Kai tsaye yaje ya shiga bude kulolin.
  Tuwon shinkafa er gote ne wanda yayi taushi da laudi har ya gaji da miyar alanyahu wacce taji qassan naman rago.
   Nan take yaji yana buqatar cin abinci sbd favourite din sa ne..
  Nan yayi zaune ya fara auna abincin hankalin sa a kwance.

  Yana cikin ci Billy ta fito domin tasa a kwashe kwanikan abinci se ta hango Hakeem yana cin abincin,
jinginawa tayi a bakin qofa tana qare masa kallo inda ta fahimci abincin ya masa dadi sosai har dai yanda ya maida hankali yana ci.



Jikin sa ne ya basa ana kallon sa ya daga ido ya hango Billy kamar wata er tsana sae kallon sa take ba ko qiftawa,yi yayi kamar bai ganta ba ya ci gaba da cin abincin sa
 Saukowa tayi ta zauna kan kujerar da ke facing dinsa tana masa wani  kallo kamar wani  masoyin ta da gaske.
   A shagwa6e ta shafa cikin ta tace"Bobby yunwa nake ji kuma oats dina ya qare,ko nazo muci tare"
  Cak Hakeem ya tsaya yana kallon yanda take shagwa6a mai cike da ban sha'awa ga duk wanda ke kallo.
   Dan guntun tsaki yayi yace a ransa"lallai yarinyar nan haukar ta sae abinda ke qaruwa ya zama dole na saita ta kar ta raina ni ganin ina cin abinda ta dafa....please Bobby kaji.
  A qufule yace"kinga malama qaddara ce tasa nake cin wannan abincin da kuma lalura kar kiyi tunanin cewa sha'awar sa tasa na zauna ina cin sa da har zaki zo kina min karuwan ci.
   Nan ya buga tsaki ya fice.
 Cike da murmushi Billy ke binsa da kallo har ya shiga daki.
   Wanda tana yin murmushin ne ganin plan dinta ya kusa fara aiki.
  Bude kula tayi ashe ya cinye tuwon kaf na cikin plate kawai ya rage,shu'umin murmushi tayi hade da girgiza kanta tace that's gud my boo-boo husband(stupid husband) naji a qaddara kaci abincin haka qaddarar zata ci gaba da janka kana cin abincin bcs d'and'anon sa da kaji ba zai ta6a baka damar sake cin wani  girkin ba sai shi..but lets see me an u who is d winner of dis game.



Sorry once again is not my fault wlh naso cika muku alqawarin da nayi amma Allah bai bani damar hakan ba but ga qarin page daya na tausar qirji🤗.



*👛18👛*

Nan ta tashi ta koma daki.

Washe gari ta hada masa lafiyayyen break fast kamar yadda ta saba.

Sannan taje tayi wanka ta shirya cikin wasu kaya riga da skirt.

Taje kan dining ta dibi quaqer oats ta zuba madara da sugar tayi zaune tana shan abinta cike da natsuwa.
  Tana cikin sha Hakeem ya fito kallo daya ya mata ya kauda kai ya fita daga cikin gidan.
   Cike da tsana ta bishi da kallo a wahalalle mai girman kai domin tasan tabbas da yunwa ya fita kasancewar kuku baya nan.


Bayan ta gama taje ta gyara masa dakin sa tsaf ta kuma wanke masa inner wears din sa da sukayi datti ta goge ta feshe su da turare ta saka a cikin wardrobe.

Guraren 3:pm kwance take tana baccin da tun 12 ta fara shi.
   cikin baccin ta ne taji Hakeem nata faman knocking cike da jin bacci ta tashi ta bude qofa wanda yayi dai dai da Hakeem ya watso mata inner wears d'in sa da ta wanke mishi.
  Cikin masifa yace"this is d last warning kar ki sake ta6a min kaya! Idan ba haka ba duk abinda na miki ke kika ja.
kuma se ki san yanda zakiyi da kayan domin ba abinda zanyi dasu!
   
_"calm down pinky,kar ki yarda plan dinki ya watse._wani  6angaren zuciyar ta ne ke tausar ta, sbd Hakeem ya kaita qololuwa ta yanda ya watso mata kayan, hakan ta dake ta qirqiro hawayen
 qarya,cikin muryar kuka mai ban tausayi ga duk wanda yaji.
  tace"haba Bobby meyasa baza ka haqura mu ajiye qiyayya, mu koma tamkar yanda iyayen mu ke so..... qarya kike sam ba hakan a ranki kawai don wata banzar manufa ce yasa kike min haka.
    _Lallai kayi gaskiya da wata manufa nake maka duk wadannan abubuwan ba don kyautatawa ba ko kuma don na kasance mata a gare ka, sae dae manufar da kake tunani sam ba ita bace_
 Tayi maganar ne a zuci kafin take cewa a fili"Bobby sam abinda kake tunani ba shi bane kawai dai yanzu na fahimci cewa qiyayya ba abu ce mai kyau ba shiyasa nake son kaima ka fahimci hakan.
  Kuma duk abubuwan da nake ma ina maka su ne a matsayin matar ka,domin samun dinbin ladar da ke tattare da hakan.....qarya kike!kuma koda da gaske kike ki sani tun ranar da aka daura auren mu na rubuta na ajiye ke ba mata ta bace sam ba aure tsakani na da ke!
  Billy taji zancen Hakeem tamkar wanda ke sanar da ita an mata bushara da gidan aljannah.
Hakeem yaci gaba da cewa amma tunda kika ce haka daga yau duk wani aikin da ke cikin gidan nan ke zaki riqa yinsa tun daga aikin kuku har kan gate man zasu ajiye aikin su ki dora inda suka tsaya, don haka tun yanzu kije ki dora min indomie na baki nan da minti goma!
  _"this guy wan kill me but zan amince da hakan bcs hakan zai qara ma plan dina qarfi domin na fahimci plan dina ya fara aiki a kansa sbd alamu sun nuna tunda ya fita ya kasa cin ko wane irin girki a waje ya kuma dawo gida ya tarar da banyi ba shi ne ya wani  dora min aikin gidan gabadaya just bcs ya riqa cin girki na!Brovo alaiki ya Billy u have really got dis drama_

Can ta dago ta kalle shi tace"shike nan zanyi duk abinda kace amma kayi haquri ka kar6i kayan nan da na wanke ma domin shima yana daga cikin aikin da zanci gaba dayi as ur wife.
    Nan ta bashi kayan a maimakon ya kar6a sae ma ya maida hannyensa baya yana kallon cikin idanun ta domin kawai ya gano ainihin abinda ke cikin ranta,Billy ta fahimci hakan shiyasa tayi saurin kauda idon ta, yace"idan da gaske kike meyasa zaki bani kayan, ai ke ya kamata ki shigar da su da kanki.
  Shiru tayi ta fahimci lallai idan tayi wasa Hakeem zai gano ainihin plan dinta, ya zama dole ta kiyaye.
   Tace"Afwan but nayi haka ne sbd naga baka son ina shiga ma d'aki anyhow,bata jira me zai ce ba tabi ta gefen sa ta mayarda kayan a mazaunin su ta fito, Hakeem kuwa yabi ta da ido yace a ransa
_"duk abinda kike shiryawa baza ki ta6a cin ma burin ki ba_ domin ko da kuskure bazan sake ta6a ko yatsar ki ba bare har nayi kuskuren wuce gun"


*Billy gir[truncated by WhatsApp]
[9/22, 6:27 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [8/7/2016] Billy giro😊:

 *```👛BILLY PINKY DURLING ```👛*



*```Na Billy giro```😊*


*```page```*
   
       *```👛19👛```*
Washe gari da asuba ta sallame sallah kenan taji Hakeem na mata knocking.
   Koda ta fito ta same shi sanye da kayan exercise yace"kije ki wanke min mota kuma kar ki 6ata min lokaci domin zan fita da qarfe takwas.

  Yana gama fada ya wuce Billy ta bishi da ido tace"da gaske yake son wahalda ni na ganin na kasa cimma burina,amma zan jure domin kaima naka lokacin zai zo da zaka shiga yanayin da baza ka iya fitar da kanka ba sae idan Allah ne ya fitar da kai,gwara ni kenan da in yanzu naso zan yakice wahalar.


Fitowa tayi harabar gidan da niyar tasa gate man yayi saurin wanke motar kafin Hakeem ya dawo daga gurin exercise.

Tsaye tayi cak tana kallon dakin gate man a rufe,
 kenan Hakeem ya sallame shi, tace" laillai in yasan wata bai san wata ba ina da numbar gateman i will call him ryt now!....Hakeem ne ya katse mata hanzari da taga ashe cikin gidan ne yake exercise inda yake zagaye gidan da jogging.
   _No prob pinky just go an wash d car zaki ci ribar hakan wata rana_.
  Zuciyar ta ce ke bata hakan ta furta "OK"a fili,
 ta shiga tunanin ta ya ma zata fara aikin da bata ta6a yi ba.
 

Komawa tayi daga ciki ta cire hijab ta dawo taje gurin motar ta dad'e tsaye tana kallon ta,
se can ta hango tiyo taje ta dauka tare da kunna fanfo ba shiri ta fara jin saukar ruwa a fuskar ta sbd kafin ta kunna fanfo bata lura da cewa bakin tiyon na facing din fuskar ta ba,a razane ta buga ihu tana ja baya yayinda ruwan ke ci gaba da watso mata a fuska har zuwa qirjin ta nan take ta jiqe kafin take fahimtar tiyon hannun ta ne ke watso mata ruwan domin ta manta cewa tana riqe da shi,
 Jefar da tiyon tayi a qasa tana sauke numfashi hade da kallon tufafin ta da suka jiqe wato riga da wando na bacci,
 rigar mai d'an siririn hannu wacce ta kai mata har guiwa wandon kuma dogo ne har qasa.
  Guntun tsaki ta buga ta kama gashin kanta ta dunqule,sannan ta duqa tana nad'e qafar wandon ta,
 sae dai tashin ta keda wuya qafar wandon ya walwale sbd sul6i ne da yadin.
   A shagw6e take kallon qafar wandon fuskar ta kamar wacce zatayi kuka tace"oh no!

Duk abin nan da take Hakeem na kallon ta yana dariya cike da mugunta.

Suna hada ido tamkar bashi ke dariyar ba yayi mata kamar sam bai ma lura da  abinda ke faruwa ba yaje kan resting chair ya zauna yana sauke gajiyar execise.


Nan taja tiyo ta tafi dashi gurin mota ta shiga watsa ma motar ruwa da taga koina ya samu taje ta kashe fanfo acewar ta gama wankin motar,domin tana kashe fanfo ta nufi qofar shiga gidan Hakeem yace ke zo nan,ba musu taje,yace me kike nufi da zaki fice baki gama wankin motar ba? Ai na gama wankin motar baka ga koinan ta ya sami ruwa ba... tsaki ya buga hade da jefa mata key yace dallah malama jeki bude gate man room ki dauko car wash da sosu ki wanke min mota!
   Nan ta duqa ta dauki makullin ta 6oye damuwar da ke qoqarin bayyana a fuskar ta, ta qirqiro murmushi tace"sorry na manta ne.


Haka taje ta bude gate man room ta dauko abubuwan wankin mota har da qyallen gogewa.

Taje tana wankin motar cike da wahala sbd ta cika kumfa sosai,ga gashin kanta ya walwale sae faman wahalar gyaran sa take.
Da qyar ta kammala tayi tsaye riqe da qugu tana sauke numfashi,Hakeem da ke kallonta yace"indai wahala ce yanxu kika soma.

Bayan ta mayarda abubuwan wankin mota a gate man room ta rufe ta kawo masa key zata fice yace"kin manta da bawa flowers ruwa ne.... cak Billy ta tsaya tana jin kamar ta fashe da kuka domin bata ta6a wahala irin ta yau ba"tace a ranta"my plan gonna kill me amma wlh sae na jure domin bazan fara wahala a banxa ba.


Nan taje ta bawa flowers ruwa tana gamawa ta fice kitchen ta hada masa break fast dinsa sbd tayi zama d'aya ta huta.

Tana gamawa taje ta cire kayan jikinta ta bawa gado amana sae sha biyu ta tashi ta shiga toilet tayi wanka taje kitchen ta dora abincin rana.


Tana gamawa taje falo tayi zaune tana kallo.
    Bata jima da zama ba ta shiga jin oda ba qauqautawa,
 tsaki tayi sbd ta rasa inda oda ke fitowa.
   Ba jinawa se ga Hakeem ya shigo gidan ransa baqiqirin ya kalli Billy da ke kwance tana hutawa Yace"be carefull kina wasa da aikin ki! kafin na bar gidan nan akwai abu biyu da bakiyi min ba,wato bani abinci da kuma bude gate sannan yanzu na dawo ina faman oda kika share ni!,, kayi haquri mantawa nayi bai ce da ita komai ba ya fice cikin 6acin rai.
   
Billy abin dariya ma ya bata tace"game din nan tamu da ban dariya take.



Hakeem kuwa da shigar sa daki ya fada toilet yayi wanka,ya shirya cikin kayan shan iska


Tana kwance taji fitowar sa ya wuce dauke da laptop yaje kan dining ya zauna ba 6ata lokaci ta bishi.

 Hakeem ya wani hakince kamar wani  Prince yana aiki da laptop Billy kuwa har ta zuba abinci a plate ta fara bashi  a baki sae dae hankalin ta baya ga bashi abinci yana kan waya tana chat da qawayen ta.
Haka Hakeem kar6ar abincin kawai yake amma hankalin sa na kan laptop bai ankara ba yaji spoon kan hancin sa,
kai tsaye ya buge spoon cike da 6acin rai duk abincin ya watse yace"dama nasan qarya kike ba gaskiya a cikin zancen ki wace mace ce zata ce tana neman lada a gun mijinta amma tana bashi abinci hankalin ta na wani  gun....sorry sorry please calm down, tabbas zance na da gaske ne,ka daina tunanin wani  abu, fatana mu kasance kamar yadda iyayen mu ke so, amma kayi haquri da kuskuren da nayi a yanzu bada niya bane" ta fadi hakane yayinda ta langwa6ar da kai ta wani  marairaice kamar da gaske.
   Hakeem bai ce mata komai ba yaci gaba da aikinsa inda yake furta cewa a ransa
_"ai kuwa kaud'in bakin ki zai ja miki domin zan maida ke tamkar house girl_
 Billy kuwa cewa take
_na fahimci kana min tsanani ne sbd na fara gajiya da hakan har ka samu ka gano ainihin  plan dina ni kuwa bazan baka wannan damar ba duk abinda zaka min zan jure bazan yarda na nuna maka gajiyawa ta ba,domin nasan sannu sannu zaka nutse a cikin plan dina_.

 Nan ta dauki wani  spoon taci gaba da bashi abinci,
 da ya gama ta kwashe kwanika ta kai kitchen bata fito ba sae da ta wanke su tas.



2 days latter .
zaune take kan bed daure da towel tana waya.
   Hakeem ne ya shigo dakin ba ko sallama tayi saurin gyara daurin towel dinta sbd yanda ta daura shi da farko ana ganin rabin mamman ta.
    Fuskar ta daure ta kalle shi bcs bata son ana shigo mata daki kai tsaye bai damu da yanayin fuskar ta ba yace"kije na fitar da kayan datti ki wanke ki goge.
  Ya fita ba tare da ya jira amsar ta ba haka ita ma bata bashi amsa ba sae ma wayar ta da taci gaba dayi.


Bayan ta gama ta saka tufafi ta dauki waya ta  nemo numbar gate man ta kira shi domin yazo ya wanke mata kayan in yaso ta biya shi.
   Domin bata jin zata iya duk da kuwa suna da washing machine.

 Bai jima ba yazo ta miqa mishi kayan dattin tace yayi sauri ya wanke ya goge kafin Hakeem ya dawo.

*Billy gir[truncated by WhatsApp]
[9/22, 6:38 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [ 8/8/2016] Billy giro😊:
*```👛BILLY PINKY DURLING```*👛




*```Na Billy giro😊```*


*```Page```*
         *```👛20&21👛```*
Gate man ya wuce ita kuma ta koma ta kwanta a nan falo daga nan sae bacci.

Tana cikin bacci ne gate man ya kawo mata kayan har ya kammala,ta kar6i kayan ta bashi kud'i ya qi kar6a!tayi tayi yaqi kar6a,
 bata yi mamaki ba sbd tasan sabon da sukayi ne yasa yaqi kar6ar kud'in bcs duk xuwan da suke dasu umma shine gate man d'in su.
  Nan taje daki ta dauko wata had'addiyar sarqar indiyawa sabuwa dal wacce da gani zata yi tsada ta hado mishi da set din en hannu ta kawo mishi tace"ya kar6i ko wannan ya kai ma matar sa, ba musu kuwa ya kar6i kayan yana ta godiya cikin harshen turanci kamar yadda ita ma take masa magana a harshen turanci.


Da ya wuce ta wuce kitchen ta duba store duk kayan abinci sun qare indomie kawai ta rage.
  Tsaki kawai tayi taje tayi kwanciyar ta domin bata jin zata iya fita ta siyo, ta maga kayan sun jima basu qare ba bcs ta siyo su ne a iya sati biyu,domin ta zaci two weeks zasuyi su koma sae taga har yanzu basu koma ba,inda ta rasa dalilin da yasa Hakeem ya wani  zauna a garin kamar wani  ma'akacin garin.

Daga haka ta koma bacci abinta.

Hakeem ne ya shigo riqe da hannun wata yarinya er 6 yrs,da gudu yarinyar taje kan jikin Billy tana fadin"didi"
   Hakan yasa Billy ta farka tana ganin yarinyar ta sake mata murmushi tace"mimi keda waye? nuna mata Hakeem tayi dake qoqarin haurawa upstairs,sannan tace"da kuma yaya Naini ya tsaya a boys quarters zai saka kayan sa,ni kuma ga nawa a bakin qofa.
   Billy da bata san makari ba ta kalli mimi a rashin fahimta tace"tare da ku zamu koma Nigeria?no didi zamu dai zauna a nan ne har su Abba su dawo... Ina suka je, cewar Billy wacce tayi maganar ne yayinda wani  d'an saurayi ya shigo ta sakar mai murmushi tace"su Naini manya ba a ganin ku duk da muna gari d'aya, ba haka bane pinky kinsan karatu muke kuma lokacin exam ya matso ko yanzu karatun ne yaja mana baza a je da mu Nigeria ba...lah su Abba Nigeria sukayi? sosai kuwa....cike da shagwa6a tace"oh no ina ma za'a je dani,wlh Allah na matsu naje naga umma,,,
 sosai shagwa6ar Billy ta bawa Naini shawa har ya jima yana kallon ta,
haka shima Hakeem dake saukowa ya kalle ta sau daya ya kauda kai tare da komawa upstairs.

   Billy tace"zasu jima sosai kenan naga har akwati mimi tazo dashi kaima kuma ka shigar da kayan ka a boys quarters?eh to baza su jima a Nigeria ba daga can sae su wuce umrah, domin tun a last month suka so suje se wani  aiki ya tsaida Abba,wanda shine ya kawo muku tsaiko kan komawar ku nigeria da wuri,
bcs baku jima da zowa ba Hakeem yaje gida yaji Abba na magana kan yana son suyi tafiya kuma baya son su bar mu,
 mu kad'ai a gida nida Mimi to anan Hakeem yace da Abba ba matsala zaku jira har su Abba suje su dawo in yaso mu kuma mu dawo gurin ku da zama.
     kenan can ne Hakeem ke zuwa kullum domin naga kamar kusan kullum sae ya fita?eh gaskiya kullum yakan je sbd wani  aiki da yake taya Abba,, ok inace dai umma bata ga laifin rashin zuwa na ba?eh to bata ga laifin ki ba, sbd cewa tayi wai ke amarya ce baki isa fitowa ba...uhm umma kenan, Allah na dai ji kunya bcs tun zuwan mu fa sau daya na kira ta a waya,ta fadi haka ne yayinda ta haura sama naini kuwa ya bi ta da ido cike da so.
 
Zan muku d'an taqaitaccen bayani game da Mimi da Naini.

Wato sun kasance 'ya'yan aminin Abban Hakeem,asalin su en kaduna ne,suna zama  new Delhi ne sbd nan mahaifin su ke aiki,suna jimawa sosai kafin su je Nigeria sbd karatun su da kuma aikin mahaifinsu wato Babban likita na fannin zuciya.
   Naini abokin wasan Billy ne sosai,amma shi ba abokiyar wasa kadai ya dauki Billy ba,soyayya mai tsanani yake mata, sae gashi kwatsam yaji tayi aure duk da yaji hakan bai daina jin sonta ba.
 ita kuwa Billy bata ma san yanayi ba,domin har yanzu a matsayin abokin wasa take daukar shi.

Wannan kenan.

Tana haurawa sama ta nufi dakin Hakeem tare da danna door bell sae da ya jima sannan ya bud'e,
 tabi ta gefen sa ta shiga tare da rufe dakin,
 Hakeem sae kallon ikon Allah yake kai tsaye ta shigo mai daki har da wani  rufewa,
 ta fahimci hakan amma ta basar tace"ba wani  abu bane dama ba kayan abinci gashi anyi baqi,,,to me yasa da kika ga ba kayan abinci bakije kin siyo ba? koda naga hakan lokaci ya qure,indomie kadai tayi saura kuma kasan Naini baya cin indomie....sae kisan yanda zakiyi da shi,
 ni kije ki hado min indomie nida Mimi,bafa komai a gidan nan da zan bashi kamata yayi kaje ka siyo kayan abinci....wani  banzan kallo ya mata yace nayi miki kama da d'an aike....oops sorry zanje d'in da kaina but kudin hannu na sun kusa qare min,bai ce mata komai ba yaje ya zaro kudi ya jefo mata, nan ta duqa ta dauka, tana dagowa suka had'a ido inda ta dawo mishi Billyn da,
 wato shaye da toka tana masa kallon kafa raina ni da yawa, a nan take kuma  ta dawo Billyn yanzu tace"to yanzu zan dafa ma indomie kafin na tafi ko? Da a tunanin ki zaki bar gidan nan baki dafa min ba!...... Mtsw!  ya buga tsakin ne yayinda Billy ta fita daga d'akin yace"oh God! meyasa su Abba suka had'a ni da ke,
 bayan baki dace da rayuwa cikin mutane ba face cikin dabbobi domin kullum daqiqancin ki sea abinda ya qaru!


Sak Billy taji abinda ya fada sbd bata riga ta rufe qofar ba tace a ranta
_"ni da kai za a ga wanda zai qare a daqiqi marar fahimta fatana kawai  Allah ya kaimu lokacin da plan dina zai gama had'uwa_
nan ta qarasa rufe qofar ta wuce.


Taje ta had'a mishi indomie shida Mimi.

Naini kuma ta kai masa abin motsa baki kafin su sayo kayan abinci a dafa mishi.


Bayan sun gama ne Billy taja Mimi da Naini suka je shopping inda suka bar Hakeem shi kadai a gida ya fito balcony yana karatun jarida.


Sun jima sosai kafin su dawo.
  Suna isowa ta fada wanka tayi shirin shiga kitchen.

White rice ta had'a da stew wacce taji naman kaji,koda ta kammala anyi magrib.

Sae da akayi isha'i sannan suka zauna ma cin abincin,
 Billy ce ta zuba musu abinci wanda kallo d'aya Hakeem ya masa yaji ransa yayi mugun 6aci,ta gefen ido Billy ke kallon shi inda take dariyar mugunta cikin ranta sbd tasan ya tsani white rice da stew, wanda tayi hakan ne da gayya sbd qin zuwan da yayi na siyo kayan abinci.
    Komai ya kasa cewa ya tashi ya bar gurin.
   Nan naini ya shiga tambayar lafiya?Billy tace"no kar ka damu may be lalura ce ta kama shi,,"ok" cewar naini daga nan yaci gaba da cin abincin sa.

Bayan sun gama cin abinci sun huta,Naini yaje 6angaren sa domin ya watsa ruwa haka Billy da mimi suka  tashi domin zuwa shirin kwanciya.


Hakeem kuwa yana shiga d'aki ya dauki makullin mota ya fita.
   

Koda ya dawo ya sami Billy da Naini kowannen su da shirin bacci, ya kalli tufafin da ke jikin Billy riga ce handless iya guiwa sae ihu take cike da murna sbd wata game din tserar mota da suke ita da naini,
Nainin da sam hankalin sa baya kan game sae Billy yake kallo wacce keyin komai cike da sha'awa.


Nan Hakeem yaje ya kashe TV Billy tayi saurin kallon shi yace"ki tashi ki koma daki kin bar Mimi ita kadai,
tashi tsaye tayi hade da bubbuga qafafun ta a qasa cike da shagwa6a tace"uhm uhm oh Bobby why!? ya zaka zo ka kashe mana tv bayan kaga yanda hankalin mu ya karkata a can, indai akan Mimi ne fa bacci ma take,but please Bobby kaga yanzu 9:30 tayi idan 10:00 tayi Allah zan koma daga ciki please Bobby kar kace a'a.

Hakeem kam shiru yayi yana kallon yanda take zuba mai shagwa6a tamkar umma ce a gabanta har da wani  buga qafa a qasa.
   Kauda idon sa yayi cike da ganin yarintar Billy ya kalli Naini wanda ya mato gun kallon Billy har ma wani  murmushi ke bayyana a fuskar shi.
    Nan ma ya kauda idon shi ya kalli Billy wacce har yanzu begging dinsa take.
    Cikin kakkausar murya ya daka mata tsawa yace"ki wuce daga ciki bana son ganin ki a nan!
   Tap idanun ta suka cika da qwallah domin ba qaramin takura ta Hakeem yayi ba, wanda duk shagwa6ar nan da ta masa tayi ne don ta samu ya barta ta qarasa game d'in ba wai don plan d'inta ba bcs at all 6acin rai ya mantar da ita kan plan d'in da take had'awa bare har ta fahimci wani  abu a ga me da Bobby kan abun da ya mata yanzu.

Sae da ta wuce ya kalli Naini wanda ransa bai masa dad'i ba kan ganin ran Billy ya 6aci.

Hakeem kuwa duk haushin naini yake ji amma haka ya da ke yace"sorry Naini i dnt mean to hurt you kasan halin ta bata san me take yi ba.


*```Billy giro😊```*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 6:41 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [8/9/2016] Billy giro😊:
*```👛BILLY PINKY DURLING ```*👛




*```Na  Billy giro😊```*


*```page```*
       *```👛22&23👛```*
Washe gari da safe Billy ce da Mimi suka sauko downstairs suka sami Hakeem da ke jiran fitowar Mimi domin ya kai ta school.


Kallon Billy yake wacce yaga idanun ta sun kumbura da alama kuka tayi kan game d'in da ya hana ta qarasa.

Girgiza kanshi yayi yace a ransa"wai ko dai yarinyar nan ta manta cewa tare da Hakeem take ba umma ba.

Mimi ce ta kula da kallon da yake ma Billy tace"yaya kai ma ka fahimci didi bata da lafiya ko?
ta6a jikin ta ma kaji yanda yayi zafi.
 Ta fadi haka ne yayinda ta riqo hannun Hakeem zata kai jikin Billy.
Cikin hikima ya hana faruwar hakan bai yarda ya ta6a jikin Billy ba sae break fast din Mimi ya kar6a a hannunta da ke cikin lunch box.
  Yaja hannun Mimi suka fita.
Yayinda Billy ta bi bayan su taje ta bude musu gate sannan ta dawo cikin gida ta fada toilet zuwa wanka.
  Ta fito ta shirya cikin doguwar riga mai dogon hannu zubin ta kamar arabian gown.

Saukowa tayi downstairs wanda yayi dai dai da shigowar Hakeem shida Naini suka nufi dining.
   Ta same su a can ta d'an saki fuska suka gaisa da Naini.
  Sannan ta zuba musu abinci.

Ta zauna kusa da  kujerar Hakeem zata fara ciyadda shi ya kar6i spoon din yace jeki yau bana buqatar hakan.
  Kallon sa tayi tace a ranta"ai dama don ka wulaqanta ni ne kace na riqa baka abinci ammà baya daga cikin aikin gidan nan...
  Me kika ce?
Da mamaki Billy ta kalle shi domin tasan maganar ta bata fito ba bare ace yaji me tace, tace"ai banyi magana ba... Kinyi magana man a cikin ranki domin yanayin fuskar ki ya nuna hakan, sanin kanki ne tun farko ke kika fara dorawa kanki lalurar gidan nan ba wani  yace kiyi ba, wanda kinyi haka ne don wata banzar manufar ki.
    Bobby ka fahimce ni mana har ga Allah manufar da kake tunani ba ita bace.
 Abinda na gaya ma d'in dai ne....
    naji da Allàh  kar ki cika mu da surutu.
   Nan Billy ta d'ibi quaker oats ta zuba madara da sugar ta wuce.
 Naini ya bi ta da kallo har ta shige daki bai janye idon shi ba.
 Hakeem da ke kallon shi yace"ya dai Naini ko wani  abu kake buqatar ta kawo ma ne?
Ajiyar zuciya ya sauke yace"no ba komai"

Daga haka sukayi shiru basu sake cewa komai ba,Hakeem sai kallon naini yake kamar wanda ke son ya fahimci wani  abu.

   Suna kammala cin abinci naini ya wuce school.


Guraren qarfe biyar Naini da Billy ne ke volleyball cike da nishadi yayinda kowannen su ke sanye da games wears sbd dama haka suke da sun had'u guri d'aya basu da aike sae volleyball.

  Suna cikin wasar ne suka ji oda Billy ta tafi cikin jogging ta bud'e gate da suka shigo ta rufe,ta koma kan wasar su.
 Naini yace ina gate man dinku da kika bude gate?
  Baya nan,
 tayi maganar ne a taqaice taja hankalin sa suka ci gaba da volleyball.
  Mimi wacce Hakeem ya dauko daga school taxo da gudu billy na ganin ta ta tarbe ta tana mata wlcm.
  Nan suka ajiye wasar suka shiga daga ciki akasin Naini da ya wuce 6angaren shi.
   Bayan Billy tayi ma Mimi wanka ta bata abinci taci kuma bata fito ba sae da ta tabbatar bata buqatar komai.

Tana fitowa ta sami Hakeem zaune a falo yana waya,
 ta fita haka yace ina zuwa?
  Ta d'an yi mamaki amma ta basar otace"zanje mu qarasa Volleyball nida Naini.....so kike ki bar Mimi ita kad'ai bayan yanzu ne dawowar ta. Game take bata buqatar fitowa.
  Ki dai koma daga ciki ba inda zakije.
  Ba musu ta koma bcs bata son ranta ya 6aci irin na jiya.


Sae dae wani abun yau kusan kwana uku Hakeem na mata abu d'aya wato yana hana ta fita suyi volleyball ita da Naini wanda ta kasa gane dalilin hakan,gashi tasan cewa ba yau ya saba ganin tana wasa da Naini ba duk zuwan da suke da su umma shine abokin wasan ta hakan yasa ta shiga dogon tunani can tace"kodai plan d'ina ya kama shi ta 6angaren da na fison ya kama shi, wata zuciyar ta ce da wuri haka?
 haka ne but ba mamaki amma yanzu xan gawada wani abu naga idan haka ne.


Nan ta fad'a toilet tayi wanka ta fito ta shirya cikin wasu en iksan tufafi, sae dai tayi matuqar kyau.
  Ta fito tana tauna chewing gum cike da natsuwa.
  Qamshin turaren ta ya bawa Hakeem damar kallon ta inda ya shiga qarewa suturar jikin ta kallo.
  Riga ce iya guiwa mai dogon hannu sae dae gabadayan ta net ce tsaf ake hango er fincikar rigar ciki wacce iya mammanta ta tsaya bata da mara ba da bz sae dan guntun wandon da ya tsaya mata iya cinya yayi mata d'as a jikin ta.
Wani  hair style ne tayi ma gashin ta mai kyau kamar wacce taje saloon.
   Tana sanye da takalma masu tsini.

Bai yi mamakin ganin dressing din ta ba sbd haka ko gida haka take abin ta idan bata fita,ma'ana iyakar ta ta zauna da shi a cikin gida domin shaqatawa.

 Tana saukowa ta nufi gun center table ta dauki key zata fita Hakeem yace"ajiye min makullin mota.
   Ba musu ta ajiya ta nufi hanyar fita yace"ina zaki je bayan kinsan Mimi awa daya ta rage naje d'auko ta daga school,
 wa kika ajiye wanda zai kula da ita?
  Ai bazan jima ba tana gama fada ta sa qafa ya sake dakatar da ita Yace"ina zaki je da en iskan kayan nan sae kace wata arniya!

Wani  irin farin ciki taji amma ta nuna 6acin rai a fili.
Ta shagwa6e fuskar ta sosai tace"Oh Bobby city beach fa zan tafi idan bansa kayan nan ba wanne kake so na sa, domin kasan ko rigar nan ta sama idan naje cire ta zanyi domin naji dadin shiga ruwa, please ka bar ni naje nan da 30mnt zan dawo.
  Wani  mugun kallo Hakeem ya sakar mata wanda yasa ta bar gurin cike da shagwa6a tana kuka.
   Hakeem bai daina kallon ta ba sae da ta shige daki ya tashi ya rufe qofa hade da zare key ya tafi da shi dakin sa.

Billy na shiga daki ta fada kan gado cike da murna tace"tabbas gayen nan ya fara sona bai sani ba that's my plan yanzu abinda ya rage na fara nuna maka so kamar da gaske but not now zan dai ci gaba da shagwa6e ma sannan daga bisani na fara nuna ma so sannu sannu kamar yadda nawa son ke shigar ka.
   Bazan qarasa plan d'ina ba har sae ka fahimci kana sona ka kuma zurfafa a ciki ta yanda rashi na zaiyi iya illata ka, ni kuma a lokacin zan zille ma na nuna ma sam ba sonka a cikin zuciya ta basaja ne kawai, na kuma had'a ma sharrin da su Abba zasu raba auren mu kai tsaye bcs abinda zan fad'a da kuma shaidar da zan bayar qwaqqarar shaida ce wacce da a raba auren da kar a raba ba aure a tsakanin mu.


Bayan kwana biyu kwance take kan bed sae juyi ta ke duk taji ba dadi tana son tayi volleyball amma tasan Hakeem zai iya hana ta tunda yana gida gashi yanzu take son suyi kafin Naini yaje lectures bcs yàu evening lectures ne da shi.

Tana nan kwance taji oda tsaki ta buga sae kuma taji dad'i Hakeem zai fita ta samu suyi wasar kafin ya dawo.


Nan ta tashi taje tana zuwa ta same shi har ya cika fam yana jiranta cikin hanzari ta  bud'e mishi gate ya fita ta rufe ta tafi 6angaren naini bata jima ba suka fito.

Suka fara volleyball.

Sun jima sosai suna yi sae taji odar Hakeem ya dawo nan taje ta bud'e mai gate ta dawo suka d'ora inda suka tsaya.

Hakeem ya fito daga cikin mota ya kalle su sau d'aya ya wuce daga ciki.

  Billy ta bishi  da ido domin tayi tunanin zai ce mata wani  Abu.

Falo yaje ya zauna yana hutawa sae yaji yana son fitowa waje ya sha iska.

Da jaridar shi ya fito yaje kan resting chair ya zauna iska mai dad'i na buso masa.

Su Billy kuwa na ci gaba da wasar su sai ihun murnar ta ake ji duk Hakeem yaji ta fara damun sa
  Hakan yasa ya dago ya kalle ta tana gudu zata d'auko qwallo cikin gudun ne accidentally qafar ta ta bugi d'ayar qafa ta fadi had'e da sakin ihu.
    Da gudu Naini yazo zai kama ta, isowar Hakeem ya dakatar da shi da cewa"barta kawai"
 sannan ya kalli Billy shaye da toka wacce ke ihu had'e da kuka yace" da Allah malama rufe mana baki duk kin bi kin cika gidan nan"cikin muryar kuka tace"Bobby wani  abu ya shige min a qafa.... naji tashi muje daga ciki...shagwa6e mai tayi kamar yarinya er shekara hud'u tace"uhm uhm Bobby bazan iya tashi
ba ji nake kamar qafata ta karye, kuma gurin da wani  abu ya shiga yana
 fitar da jini sosai"
 ta fadi hakane yayinda ta nuna mai yaga tabbas ba wasa jini ke fita a gurin.
   Ya durqusa gab da ita yana qarewa gurin kallo kamar wani  doctor, nan ya fahimci d'an wani  dogon kare ne kaurin sa da tsayin sa zai kai stick d'in ashana,gashi kad'an ya rage ya qarasa shigewa cikin qafarta.
   A hankali yakai  hannun sa gun,
 Billy ta jaye qafar da sauri tana kuka had'e da yarfi da hannu ta kalle shi da idanun ta da ke ta zubar da hawaye tace"Bobby Allah ciwo nake ji sosai muje daga ciki tukun ko za a cire"
   Kauda idon sa yayi gefe yana tunanin to ya zai yi,kallon naini yayi kafin yake maida duban sa gun Billy yana kallon ta kamar mai wani  shawara a ransa.
  A hankali naga yakai  hannun sa ya d'auki Billy cak,wanda yayi dai dai da saukowar ruwan sama, bai yi mamaki ba domin yasan da hadarin, kallon Billy yayi wacce tayi saurin cusa fuskar ta a qirjin sa, sbd ko kad'an bata son jin saukar ruwan sama a jikin ta, yayi second biyar yana kallon ta sannan ya kama hanya.
  Naini kuwa kallon su yake kamar wanda zai yi kuka har suka shige daga ciki.

*```Billy giro😊```*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 6:44 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [9:14PM, 8/11/2016] Billy giro😊:
*👛BILLY PINKY DURLING👛*


*Na Billy giro😊*


*Page*
 

    *👛25 to 28👛*
Da dare bayan har sunyi shirin kwanciya ba su riga sun kwanta ba,sbd zaune suke kan bed amma Billy har ta kwanta Mimi kadai ce a zaune tana shan cornflakes sbd yau Billy bata iya dafa musu abincin dare ba.


Knocking suka ji,
Billy tace "yes come in"

A hankali Hakeem ya bude qofar ya shigo dauke da leda biyu a hannun sa,
  Yakai d'aya kan drawer ya ajiye sannan ya bawa Mimi dayar"ya shafo fuskar ta tare da fadin sorry Mimi Allah na manta cewa yau baza mu sami dinner ba"no ba komai yaya.
  Nan ya bude ledar gasasshiyar kaza ce da fresh milk yace sae ki fara ci ko, kallon Billy tayi tace"Didi zo muci"
no bacci nake ji bazan iya cin komai ba yanzu, amma didi fruits kawai naga kinsha fa,don't worry ci kawai kinji"
 ta fadi haka ne yayinda ta juya musu baya ta qara jan blanket d'in jikin ta.

Mimi tace"pls yaya muci tare domin bana jin dad'in ci ni kad'ai.

Ba musu yasa hannun sa suka ci.
  Bayan sun gama ne Mimi ta tashi ta nufi toilet, shi kuma ya tashi zai bar dakin ya kalli Billy wacce tuni baccin ta yayi nisa yaje ya dauke ledar da ya ajiya kusa da ita kan drawer,
 ya saka a fridge yayinda Mimi ta fito toilet ta kwanta.

shi kuma ya fita hade da kashe wutar d'akin.
Washe gari da asuba  Hakeem ne ya dawo daga  masallaci,
yaje dakin Billy yana knocking bai shiga ba sae da Billy ta bashi izini.

Ya shigo yayinda Billy ta 6alla wutar d'akin had'e da yaye blanket dinda ke jikin ta.
  Ta tsure qafar ta da kallo kamar yadda Hakeem ke kallon,
 qafar nan yagà ta qabe sosai.

Kauda idon sa yayi yace"kinyi sallah kuwa?
 shiru ta mishi domin tasan fashin sallah ta ke haka shima bai ce mata komai ba face"idan kin gama bacci anjima doctor zai zo ya duba qafar, ta gyada mai kai kafin yake  fita.
  Ta koma ta kwanta.

Da yake yau weekend ba zancen tada Mimi tayi shirin zuwa school.


Sae guraren qarfe goma ta farka ta samu ta lalla6a ta shiga wanka ta shirya sannan ta tada Mimi ita ma tayi wankan.

Gabad'ayan su gidan da tea sukayi break fast,suka had'a da d'umamen leda biyu na gasasshiyar kazar jiya wacce Billy bata ci ba da ta kuma Hakeem.


Bayan sun gama ne Hakeem ya kira doctor, koda doctor ya duba qafar ya fahimci tayi targad'e.
  nan doctor yace da Hakeem sae fa anja qafar,no ba komai kayi duk abinda kake ganin ya dace.
   Duk suna magana a harshen hausa ne kasancewar doctorn bahaushe ne aiki ya kawo shi new Delhi asalin sanin sa da sukayi shine doctorn Abban Hakeem,tun a Nigeria.


Nan doctor ya kai hannu yana qoqarin fara jan qarfar,
 Billy tayi saurin kallon Hakeem tace"please Bobby ni kawai ya ban magani gurin ya warke ba sae an ja ba, Hakeem bai ce mata komai ba yayi kamar ma bada shi take magana ba face doctor da ya ce, dole sae anja domin daidaita qashin da yaje inda bai dace ba.
  Ba yanda ta iya amma ji take kamar ta fara kurma ihu kafin aja qafar.

  Nan ya fara jan qafar a hankali tun tana jaquri har ta fara sakin ihu,ta kama pillow ta matse sosai kamar wacce ke shirin raba shi biyu,kuma duk ta wani  cusa fuskar ta a ciki yayinda ta shiga  roqon a barta ta huta tukun.
  Hakeem yace da doctor barta d'in ta huta but idan zaka sake jan qafar ka mata  zama d'aya domin ka huta da ihun ta....no Bobby kar ya min zama d'aya Allah zan iya mutuwa,Hakeem bai ko kula ta ba sae ma fita yake qoqarin yi daga d'akin.
 Doctor yace"da dai ka barta a mata a sannu d'in sbd qafar ta kwana ba a ja ba, akwai zafi sosai.
  kawai kayi yanda nace.
 yana gama fad'i ya tafi d'akin shi ya dauki laptop ya zauna ya bud'e haka sae ya tsaya cak sbd ihun Billy da yaji sau d'aya bata sake ba.
      Tashi yayi yaje d'akin ya sami Billy  ta sauka kan bed tana faman yarfi da hannu tana wahalallen
Kukan da ko sautin sa baya fita.
  Hakeem ya maida dubansa gun doctor yace hope ka kammala?yace eh tare da rubuta masa maganin da zai siyo mata tasha sannan ya tarkata kayan sa ya bar gidan.

Hakeem ya kalli Billy da ke jingine jikin bed ta dora kai kan guiwoyinta tana ci gaba da kuka.

 Har zai fita daga d'akin sae kuma yaje gab da ita ya durqusa har yana shaqar qamshin turaren ta wanda yasa ya d'an ja baya kad'an sbd wani  dalili nashi.
  Yace kinga malama kukan ya isa haka idan ba so kike kija ma kanki wani  ciwon ba.
  Dagowa tayi tana kallon shi da idanuwan ta da suka cika tap da qwallah yana kallon cikin idon ta,
 yayi saurin jaye idon shi a hankali sae kuma ya sake kallon ta yace"mene ne?
le6ace baki kawai tayi ta fashe mishi da wani  sabon kuka mai cike da shagwa6a.
  Sauke ajiyar zuciya yayi a hankali ya tashi ya fita daga d'akin.

Ya fito falo ya sami Naini da Mimi tana zuba mishi surutu shidai ko kula ta baya yi,bcs yanayin sa suku suku kamar mai wani  tunani.
  Yana ganin Hakeem yace ko zan iya zuwa naga pinky? Ba yabo ba fallasa ya kalle shi kafin yake cewa "eh".

  Nan suka haura sama shida Mimi shi kuma Hakeem ya fita daga gidan.


Bai wani  jima ba ya dawo ya zarce sae dakin Billy d'auke da magunguna a hannun shi,ya ajiye maganin  kan drawer yace ki duba kowanne da akwai yanda zaki shashi a rubuce.
 
Sannan ya kalli Naini wanda ke kallon Billy tana share hawaye zata koma kan bed ta zauna.

Yace"Mimi kuzo muje falo"nan suka tashi suka bar Billy ita kadai,wacce bata bi ta kan magani ba sae kwanciyar ta da tayi.



Haka ta yini kwance sae da dare ta d'an ji sauqin qafar ta,ta tashi kenan mimi tace "Didi tun dazu fa yaya ya kawo wata leda inaga abincin ki ne,sbd mu har munci namu"ok bari nayi brush.

Tana shiga toilet,sae ga
 Hakeem yayi knocking Mimi ta bud'e mai tare da fad'in "didi ta tashi amma ta shiga toilet zata yi brush"
 no nazo ne naji ko kinci naki abinci eh yaya nayi jiran ka har na gaji shine mukaci nida yaya Naini,yace "ok" ya juya zai bar dakin.

Ita kuwa Billy Koda ta shiga toilet se taji tana buqatar ta watsa ruwa a nan toilet corner ta cire kayan jikinta
 ta daura towel ta qarasa shiga toilet tare da yaye towel ta ajiye a mazaunin shi,
 zata shiga gurin wanka kenan sae kawai wutar toilet d'in ta d'auke ihu ta saki tana mai lalabar towel d'in ta.

 Hakeem da ke qoqarin fita daga d'akin ya tsaya cak yana sauraren yanda billy ke faman ihu kamar wacce taga abin tsoro bcs akwai wuta a dakin ta toilet kad'ai ta d'auke.

  Toilet d'in ya shiga domin ganin mene ne sae kawai wutar ta kawo.

Yayi tsaye yana kallon Billy wacce ta rufe fuskar ta da towel wanda ya sauko tun daga kan fuskar ta har zuwa cinyoyinta ya rufe,
 sae ihu take saki taqi d'agawa koina kuma taqi bud'e fuskarta bare ta fahimci wutar ta kawo sae can taji kamar mutum ya shigo ta fara jaye towel d'in a hankali har ta bud'e fuskar ta.
   Tana ganin Hakeem ta qara danne towel d'in da ke kan qirjinta  had'e da turo baki tace"to ni ka fita ka wani  tsaya kana kallo na"
  Kauda kansa yayi yayinda d'an guntun murmushi ke son bayyana a fuskar sa,yace a ransa"wai meyasa nake son childish behavior nata.. bcs hakan na mata kyau sosai,
 cewar 6angaren zuciyar sa,yace"no ba haka bane nida komai nata baya birge ne bare naga tamin kyau har nayi sha'awar hakan, its just bcs inajin nishadi a yau.

Nan ya gama zancen zucin sa ya fice Billy tayi murmushi had'e da girgiza kanta tace"za dai ka gano ne nan gaba.


Bayan ta fito daga wanka ta d'auko Vaseline tana shafawa,Mimi tace"didi kar ki shafa mai kan qafar ki mai ciwo bcs akwai wani  magani da naga uncle ya shafa miki kina bacci"
   Billy tayi fari da ido tace
_"a ranta amazing yanzu har hakan ta fara faruwa  tsakani na da  Bobby"_
Sannan tace da Mimi a u sure? Allah kuwa didi, kingan shi ma,
 ta bude ledar magungunan da Hakeem ya ajiye a dazu ta dauko mata maganin,
 tube ne d'an qarami da shi,ta dubi instruction nashi sau uku ake shafa shi a rana ta matsa maganin ta fara shafawa yayinda fuskar ta ke d'auke da murmushin da ita kadai ta baiwa kanta sani.
 
Bayan ta gama shiri ne ta bud'e ledar abincin ta,
 snacks ne a ciki da gasasshiyar kaza.

 Ta tashi da d'an d'ingishin ta taje ta bud'e fridge ta dauko freshmilk tayi sanyi har ta gaji taje ta zauna taci abinci tasha magani.

Bayan kwana biyu da faruwar haka qafar Billy tayi sauqi sosai domin har girki ta ci gaba da dora musu.
 

Hakeem,Naini,Mimi sune zaune kan dining Billy na zuba musu abincin dare.
  Fried rice ce wacce taji spices taji komai yanda ya kamata sae qododi dake yawo cikin ta.

Hakeem ya kalli abincin sau d'aya ya kauda kai"yace wai ke meyasa long time kin daina min favourite food d'ina?da mamaki ta kalle shi domin tasan ko wannan favourite food d'insa ne tace"kamarya?i mean tuwon shinkafa da miyar ganye... oh yes naga baka son ayi maka tuwo da wata shinkafa face er gote kuma dama er goten da kaga ina yi maka tuwo da ita a kwanaki wacce su umma suka ta6a bari ce wani  zuwan da mukayi kafin wannan,
 kuma ba wani  yawa ne da ita ba bcs kasan its just bcs of u ake zowa da ita.
  Ajiyar zuciya yayi cike da damuwa Yace olryt.
   Nan yaja plate suka fara cin abinci shida Mimi.
Naini kuwa shi kadai yake cin abinsa haka ita ma Billy amma farfesun kaji ne take sha.

Haka rayuwar su taci gaba yayinda yanzu Hakeem komai yaga Billy  tayi sae yaga hakan ya bashi sha'awa amma yaqi yarda da abin da zuciyar sa ke son raya masa na cewa he is in love wit her,,, just ya d'auki abun a zaman da suke guri d'aya ne ya kawo hakan.
   Sbd yanzu duk inda Hakeem yake,sae Billy tayi qoqarin ganin tana gurin,sbd qarawa plan d'in ta qarfi wanda
   ko school Hakeem zai kai Mimi sae Billy tayi ta begging d'in sa cike da shagwa6a kan zata yiwa Mimi rakiya.
   Shi kuwa Hakeem shagwa6ar da Billy keyi mishi kesa ko yayi niyar dizgata se ya sami kansa da kasawa hakan yasa yake zuwa da ita wanda har suje su dawo ba mai ce ma wani qala sae idan Billy ce tayi magana.


Kwance yake a falo kan sofa sanye da singlet da three quarter da alama bashi da lafiya domin alamu sun nuna hakan.

Billy ce ta sauko downstairs sanye da riga pink handless wacce tsayin ta bata qarasa kai mata a guiwa ba,
 tazo ta zauna qasa kusa da kujerar da Hakeem ke kwance idanun sa a lumshe suke amma Billy na zama ya bude su a hankali,ta sakar mai sexy eyes d'inta tace"zakaci wani  abu kafin doctor yazo?um um bana jin yunwa ruwa kawai nake son sha.
  Nan ta tashi ta kawo mishi ruwa bai kar6i ruwan ba sae da ya tashi zaune yayinda Billy ta bashi ruwan,sai da yasha sannan ya koma ya kwanta.
    Billy ta wani  nuna damuwa sosai a fuskar ta tana mishi sannu kamar da gaske.
  Kallon ta kawai yayi bai ce da ita komai ba Yace"ki tashi kije daga ciki doctor na kan hanya kuma kinsan bai kamata yazo ya ganki da kayan da ke jikin ki ba"
   Ba musu ta miqe yayinda Hakeem ya shiga tsananin mamakin kansa da furta hakan, meye damuwar shi koda a tsirara doctor zai ganta,wata zuciyar tace ka furta haka ne kawai sbd ita musulmace haramun ne wani wanda ba muharramin ta ba ya ganta haka.
 

Billy kuwa cike da sh'umin murmushi ta shiga d'aki sbd ta fahimci yanda Hakeem ya shiga mamakin kansa sosai.

Zuge zip din rigarta tayi ta cire rigar ya zamo daga ita sae pant ta jawo towel ta daura sbd wanka take so tayi amma bata shiga wankan ba ta tsaya gyaran d'aki.

 

A 6angaren Hakeem kuwa Billy na tashi sae ga doctor.
  Sai da suka d'an gaisa
  yace da Hakeem me kake jin yana maka ciwo a jikin ka? Kawai ka duba ni doctor bcs bansan ainihin abinda ke damuna ba.
  Nan ya shiga dube duben shi a jikin Hakeem inda yake mishi wasu tambayoyi yana bashi amsa.
  Bayan dube duben shi da jin amsoshin Hakeem,
 sae yayi shiru kamar mai mamaki har yana d'an jinjina kan sa,
can dai ya dafi kafad'ar Hakeem ya fara magana cike da natsuwa yace"Hakeem  ba wani  abu ne ke damunka ba face tsantsar sh'awa!

da mamaki Hakeem yace as how doctor? I mean kana buqatar kasancewa da mace!

Hakeem ya qara jin
 zancen wani  iri yayi murmushin yaqe yace"doctor bancin matar da nake da,
 sae na nemo wata macen? Hakeem kenan kar ka manta kana tare da doctor ne,domin a binciken da nayi na fahimci sha'awar da ke dauke da kai ba alamar  ka kusanci mace nan kusa ma'ana ka jima sosai baka kusanci matar ka ba!

kan Hakeem ne ya kunce domin shi a iya sanin sa bai ta6a jin yana buqatar mace ba, bare shi da ke tare da Billy ta ya zai sakawa kansa buqatar mace bcs Billy fanko ce ba abin sha'awa bace,kawai dai yasan idan ya shaqi qamshin turaren ta yakan ji wani  yanayi a jikin sa har dai idan tana kusa da shi, haka idan tana mishi shagwa6a ji yake kamar ya rungomo ta yana lallashin ta...doctor ya katse shi da cewa Hakeem ya kamata ka ajiye wata qiyayya da girman kai,ka kar6i abinda kake buqata a gurin matar ka,idan ba haka ba sha'awar nan zata kai ga illata ka..... Pls doctor ka daina wannan zance  bcs even yesterday night I slept with my wife ta ya zaka ce wani  sha'awa ce ke damuna!

 D'an guntun
 murmushi doctor yayi yace a ransa.
_nayi boko  kayi boko baza mu nuna wa junan mu wani  abu ba,but zan nuna ma nafika yawan shekaru na kuma nuna ma ba abu d'aya muka karanta ba_

Yace "shikenan kayi haquri da nayi ma rashin fahimta amma ina zuwa,
 nan ya tashi ya fita bai wani jima sosai ba ya dawo,
yace da Hakeem ga wannan magani kasha,
 magani ne wanda idan an kasa gane ainihin matsalar mutum idan ya sha shi inshaAllah zai ji sauqi,
  Ba musu Hakeem ya kar6i tablet d'in yasha.
  Yayi minti d'aya da shan maganin,
yace doctor maganin nan jiri yake sawa ne?
sorry ba jimawa zaka daina jin haka but idan ba damuwa ko zaka kira min pinky nayi mata en wasu tambayoyi a game da ciwon ka?

Da qyar Hakeem ya iya ce mishi ba damuwa"  sbd wani yanayi da ya fara jin kanshi,
nan ya tashi ya  tafi sae tangad'i yake kamar wani mashayin da yasha ya fara buguwa a haka har ya shiga d'akin Billy.

Doctor ya girgiza kansa yace a ransa"lallai Hakeem da pinky duk da had'a ku auren  da aka yi bai sa kun haqura kun shirya kanku ba,
amma ba komai na kusa kawo qarahen abun,domin wannan maganin da kasha ba zai ta6a baka damar fitowa a dakin pinky ba har sae ka kusance ta!
  Yana gama fad'ar haka ya fita daga gidan.

Hakeem kuwa yana shiga d'akin Billy....

*Billy giro😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 6:47 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [ 8/15/2016] Billy giro😊:
*👛BILLY PINKY DURLING👛*


*Na*

*Billy giro😊*

*page*
    *👛33&34👛*
Hannun ta ya ajiye a hankali hade da fitar da ajiyar zuciya, ya d'an kauda kansa gefe ya kuma sake kallon Billy wacce har yanzu idon ta yana kanshi.
   Idanun ta ne suka ciko tap da qwallah sbd rad'ad'in bala'in da take ji a qasan ta, ta shiga kallon yananyin d'akin cike da mamaki yayinda hawaye ke qoqarin gangarowa kan kumatun ta,cike da damuwa Hakeem ya d'an matsa kusa da ita tare da riqo hannun ta kamar mai son cewa wani  abu.
  Billy kuwa cikin muryar kuka tace"Bobby me yake faruwa da ni ne?
Shiru Hakeem yayi ya rasa me zai ce da ita, domin ko kad'an baya son tasan dalilin faruwar hakan.
  Hannun ta da yake riqe da shi ya ke faman  murzawa a hankali cike da tunanin me zai ce mata.

Sautin kukanta ne ya dawo dashi,
 yayi saurin kallon ta hade da girgiza mata kai alamar ta daina kuka.
  Cike da shagwa6a ta fizge hannunta da yake faman murza tace"to ni ka sanar dani me ya faru dani har ka kawo ni asibiti?
cikin muryar lallashi abinda bai ta6a yi mata ba yace"shi kenan kukan ya isa haka kiyi shiru idan kina son na sanar da ke kinji, nan ta share hawayen ta kamar  wata er baby tace"to fad'amin ina jinka, um um ni bazan gaya miki ba sae kinci abinci tukun, yayi maganar ne tamkar da qaramar yarinya yake magana kuma yana sane yayi hakan just bcs ya samu ya lalla6a ta.
  Bata ce da shi komai ba har ya tashi ya fita daga d'akin.

 Bai wani  jima ba ya dawo  dauke da leda a hannun sa,ya sami Billy sae qoqarin tashi zaune take cike da son tayi kuka,cikin hanzari Hakeem ya qarasa gurinta yace"mene ne?ina so na zauna amma inaji kamar bazan iya ba,
lumshe idonshi yayi a hankali ya ajiye ledar da ke hannun sa,ya taimaka mata ta zauna.
Sannan ya dauko ledar da ya shigo da ita ya bud'e ba wani  abu bane face snacks da danqwaleliyar gasasshiyar kaza yakai  gaban ta ya ajiye ta tsure abincin da ido kawai ba alamar zata ci.
  Ganin haka yasa ya gutsura naman kaza ya kai mata a baki bata bud'e bakin ta ba sae kallon sa take kamar mai magana cikin ranta,can ta bud'e bakin ta a hankali ya saka mata.
  Da haka yaci gaba da ciyar da ita har sae da tace ya ishe ta.
  Nan ya tsiyaya ruwan lemu fresh one ya bata,wad'an da dama akan kawo ma patients su had'e da abinci amma sanin bata cin abincin ya siyo mata wani .
  A hankali ta koma ta kwanta yasa top bedsheet ya rufa mata har zuwa qirjinta.
   Billy sae kallon sa take kamar wani  baqon ta tace"Bobby baka gaya min ba,bari kiyi bacci tukun kinji.
  Kamar zata ce wani  abu sae kuma ta fasa.


  Sannu sannu kuwa ta fara jin bacci na fizgar ta har ta rufe idonta.
  Hakeem kuwa yana tsaye a kanta kamar wani bodyguard sae can ya zauna wanda yayi dai dai da shigowar doctor.
  Doctor yace ya ake ciki ta koma bacci ne? Eh, ok inace ka sanar da ita dalilin zuwan ta asibiti domin nasan da tashin ta ta buqaci jin hakan,
  Ban sanar da ita ba domin bansan a ya zata d'auki abun ba... Kaga ka sanar da ita kawai meye a ciki,matar ka ce fa, sae dae kuskuren ka d'aya girman kan da kasa na qin sanar da ita buqatar ka kaje ka saka mata maganin bacci a ice cream domin ka biya buqatar ka, ba tare da ta sani ba, wanda nasan jin hakan ne kad'ai zai 6ata mata rai, amma ai kai namiji ne zaka iya shawo kanta idan kaso,, sae da ya nisa sannan yace haka ne doctor zan gwada yin hakan.
   Duk maganar nan da sukeyi sak a kunnen Billy wanda ta tsinci kanta cikin tashin hankali har ta qagu doctor ya fita.

Fitar sa keda wuya ta yaye bedsheet d'in jikin ta ta jefar da shi,ta kalli Hakeem cikin tsananin tashin hankali hawaye wani na bin wani  bakinta na rawa tace"innalillahi wa inna ilaihi raji'un!
 Bobby cin amanar da kamin kenan!
ka rabani da budurci na domin kawai ka lalata min rayuwa!
   Cike da son yi mata bayañi ya tashi yayinda
ta wani sauka kan bed da qarfi kamar ba wacce akayiwa aiki ba.. Hakeem yace"No ba fa haka bane saurare ni kiji....a fusace taci kwalar shi tace"me zanji! me zaka ce dani! bayan ka lalata min rayuwa!why Bobby! why baka kashe ni ba a lokacin da ka gama keta min haddi!?why!?
da sauri Hakeem ya rungumo ta sbd yanda take jijjiga jikin ta sosai, gashi yana gudun ta jiwa kanta ciwo, yace"nifa ban kusance ki ba ki saurareni kiji.... Qarya ne!
ta fad'i haka ne yayinda ta fizgi jikin ta daga nashi taci gaba da cewa"bcs wannan rad'ad'in da nake ji a qasa na bazai ta6a bani damar yarda da zancen ka ba!azzalumi macuci wlh sae Allah ya isar min
domin bazan ta6a yafe maka ba!

"Ya salam"
 cewar Hakeem wanda yaji komai ya cakud'e masa,
Sae ga wani tashin hankali wato  hango jini na sauka a qafafun Billy, domin da qarfi ta fizge kanta  daga jikin Hakeem.

Kafin Hakeem yace komai sae ga doctor ya shigo cikin sauri sbd jin hayaniya,doctor yace"subhannallah! Hakeem ya akayi haka ta faru? cikin rud'u Hakeem ke kallon doctor ya rasa me zai ce da shi,doctor ya kalli Billy wacce ke kuka sosai mai tsima zuciya,jini na faman sauka a qafafunta,cikin kuka ta durqusa kan guiwoyinta ba tare da ta damu da jinin da ke fita a jikin ta ba,
 sae maganganu take kan Hakeem ya cuce ta.

Wanda nan Doctor ya fahimci komai,yaje gab da ita yana so ya mata bayani yanda abun yake....tayi saurin sa hannu ta rufe kunnuwanta tace"bana son jin kamoi doctor! bana so!domin naji komai a kunne na kuma naji a jikina da gaske ne abun,domin inajin zafin rad'ad'in abinda ya min!

Tana gama fad'a ta share hawaye da takaici ta nufi hanyar fita daga d'akin kamar wata zautacciya, Hakeem yayi saurin kamo ta,doctor Yace"dora ta kan bed ayi mata allurar bacci"

Da qyar Hakeem ya d'ora ta domin sae fizge fizge take tana kai mai cizo ta koina wanda da qyar doctor ya samu ya mata allura.

A tare suka sauke ajiyar zuciya cike da damuwa.

Nan doctor ya fita sae gashi ya dawo tare da wata baindiya wato likitar da tayiwa Billy aiki,
Nan doctor yaja Hakeem suka fita waje.

 Zaune Hakeem yake amma kwata kwata hankalin sa baya gurin sae halin da Billy take ciki yake tunani..... Wayar sa ce tayi qara koda ya duba Naini ne,maida ta kawai yayi a aljihu domin baya jin zai  iya receiving call a halin da yake ciki,yana ji tana ta faman ruri har ta tsinke.

Docta na fitowa Hakeem ya miqe da hanzarin sa  ta dakatar da shi kan cewa bazai sami shiga yanzu ba domin ana buqatar Billy ta sami hutu sosai.

Jiki sanyaye yaje ya zauna sae dai ya kasa zama ya kasa tsayi har sae da yaje nan wani guri da ake hango mutum ta jikin glass ya leqa inda yaga ancanza mata uniform din jikin ta ancire wad'an da suka 6aci da jini har bedsheets d'inma duk an canza,ya jima yana kallon ta sannan ya koma ya zauna tare da zaro wayar sa ya kira Naini sukayi magana.

Sai gashi ba a wani  jima ba yazo hankali tashe duk yabi ya shiga damuwa.

Da qyar Hakeem ya samu ya kwantar mai da hankali kan cewa ba wani  abu bane.


Sae da ta tashi daga bacci ne aka basu damar shiga wanda a lokacin har Hakeem yaje ya d'auko Mimi daga school.

In banda kuka ba abinda Billy keyi,
 Naini yayi iya qoqarin sa na ganin ta daina kuka tayi magana amma taqi haka ko Mimi,
 bare shi Hakeem da baya ko son yayi magana ta hau shi da masifa kan abinda bai riga ya aikata ba.


Washe gari  aka sallame ta,suka koma gida.

Har akayi kwana biyu Billy bata da aiki sae kuka duk tabi ta rame lokaci d'aya.
   Sosai Hakeem ya shiga damuwa ya rasa ta yanda zai yi ya rarrashi Billy domin ya samu ya fahimtar da ita.

Guraren qarfe biyu na dare Hakeem ya fito daga d'akin shi sbd yaji fitowar Billy,
 yana kallo taje kan two seater ta zauna wacce yaga har yanzu tana cikin qunci sosai,sae faman share hawaye take domin yanzu aikin kenan,kamar daga sama yaji ta fashe da wani  sabon kuka ta hade kai da guiwa.

Sosai kukan ya ratsa jikin Hakeem,ya koma dakinsa cike da damuwa ya d'auko wasu takardu kamar na asibiti.


Ya sauko downstairs gaban Billy ya durqasa kan guiwoyinsa kafin yace komai ta d'ago sbd motsin da taji ta kalli Hakeem da yayi kneel down a gaban ta,sae kawai taga ya kama kunnen sa yace"please am sorry *Pinky*,am so sorry.

*Billy giro😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 6:54 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [ 8/15/2016] Billy giro😊:
*👛BILLY PINKY DURLING👛*


*Na*

*Billy giro😊*

*page*
    *👛33&34👛*
Hannun ta ya ajiye a hankali hade da fitar da ajiyar zuciya, ya d'an kauda kansa gefe ya kuma sake kallon Billy wacce har yanzu idon ta yana kanshi.
   Idanun ta ne suka ciko tap da qwallah sbd rad'ad'in bala'in da take ji a qasan ta, ta shiga kallon yananyin d'akin cike da mamaki yayinda hawaye ke qoqarin gangarowa kan kumatun ta,cike da damuwa Hakeem ya d'an matsa kusa da ita tare da riqo hannun ta kamar mai son cewa wani  abu.
  Billy kuwa cikin muryar kuka tace"Bobby me yake faruwa da ni ne?
Shiru Hakeem yayi ya rasa me zai ce da ita, domin ko kad'an baya son tasan dalilin faruwar hakan.
  Hannun ta da yake riqe da shi ya ke faman  murzawa a hankali cike da tunanin me zai ce mata.

Sautin kukanta ne ya dawo dashi,
 yayi saurin kallon ta hade da girgiza mata kai alamar ta daina kuka.
  Cike da shagwa6a ta fizge hannunta da yake faman murza tace"to ni ka sanar dani me ya faru dani har ka kawo ni asibiti?
cikin muryar lallashi abinda bai ta6a yi mata ba yace"shi kenan kukan ya isa haka kiyi shiru idan kina son na sanar da ke kinji, nan ta share hawayen ta kamar  wata er baby tace"to fad'amin ina jinka, um um ni bazan gaya miki ba sae kinci abinci tukun, yayi maganar ne tamkar da qaramar yarinya yake magana kuma yana sane yayi hakan just bcs ya samu ya lalla6a ta.
  Bata ce da shi komai ba har ya tashi ya fita daga d'akin.

 Bai wani  jima ba ya dawo  dauke da leda a hannun sa,ya sami Billy sae qoqarin tashi zaune take cike da son tayi kuka,cikin hanzari Hakeem ya qarasa gurinta yace"mene ne?ina so na zauna amma inaji kamar bazan iya ba,
lumshe idonshi yayi a hankali ya ajiye ledar da ke hannun sa,ya taimaka mata ta zauna.
Sannan ya dauko ledar da ya shigo da ita ya bud'e ba wani  abu bane face snacks da danqwaleliyar gasasshiyar kaza yakai  gaban ta ya ajiye ta tsure abincin da ido kawai ba alamar zata ci.
  Ganin haka yasa ya gutsura naman kaza ya kai mata a baki bata bud'e bakin ta ba sae kallon sa take kamar mai magana cikin ranta,can ta bud'e bakin ta a hankali ya saka mata.
  Da haka yaci gaba da ciyar da ita har sae da tace ya ishe ta.
  Nan ya tsiyaya ruwan lemu fresh one ya bata,wad'an da dama akan kawo ma patients su had'e da abinci amma sanin bata cin abincin ya siyo mata wani .
  A hankali ta koma ta kwanta yasa top bedsheet ya rufa mata har zuwa qirjinta.
   Billy sae kallon sa take kamar wani  baqon ta tace"Bobby baka gaya min ba,bari kiyi bacci tukun kinji.
  Kamar zata ce wani  abu sae kuma ta fasa.


  Sannu sannu kuwa ta fara jin bacci na fizgar ta har ta rufe idonta.
  Hakeem kuwa yana tsaye a kanta kamar wani bodyguard sae can ya zauna wanda yayi dai dai da shigowar doctor.
  Doctor yace ya ake ciki ta koma bacci ne? Eh, ok inace ka sanar da ita dalilin zuwan ta asibiti domin nasan da tashin ta ta buqaci jin hakan,
  Ban sanar da ita ba domin bansan a ya zata d'auki abun ba... Kaga ka sanar da ita kawai meye a ciki,matar ka ce fa, sae dae kuskuren ka d'aya girman kan da kasa na qin sanar da ita buqatar ka kaje ka saka mata maganin bacci a ice cream domin ka biya buqatar ka, ba tare da ta sani ba, wanda nasan jin hakan ne kad'ai zai 6ata mata rai, amma ai kai namiji ne zaka iya shawo kanta idan kaso,, sae da ya nisa sannan yace haka ne doctor zan gwada yin hakan.
   Duk maganar nan da sukeyi sak a kunnen Billy wanda ta tsinci kanta cikin tashin hankali har ta qagu doctor ya fita.

Fitar sa keda wuya ta yaye bedsheet d'in jikin ta ta jefar da shi,ta kalli Hakeem cikin tsananin tashin hankali hawaye wani na bin wani  bakinta na rawa tace"innalillahi wa inna ilaihi raji'un!
 Bobby cin amanar da kamin kenan!
ka rabani da budurci na domin kawai ka lalata min rayuwa!
   Cike da son yi mata bayañi ya tashi yayinda
ta wani sauka kan bed da qarfi kamar ba wacce akayiwa aiki ba.. Hakeem yace"No ba fa haka bane saurare ni kiji....a fusace taci kwalar shi tace"me zanji! me zaka ce dani! bayan ka lalata min rayuwa!why Bobby! why baka kashe ni ba a lokacin da ka gama keta min haddi!?why!?
da sauri Hakeem ya rungumo ta sbd yanda take jijjiga jikin ta sosai, gashi yana gudun ta jiwa kanta ciwo, yace"nifa ban kusance ki ba ki saurareni kiji.... Qarya ne!
ta fad'i haka ne yayinda ta fizgi jikin ta daga nashi taci gaba da cewa"bcs wannan rad'ad'in da nake ji a qasa na bazai ta6a bani damar yarda da zancen ka ba!azzalumi macuci wlh sae Allah ya isar min
domin bazan ta6a yafe maka ba!

"Ya salam"
 cewar Hakeem wanda yaji komai ya cakud'e masa,
Sae ga wani tashin hankali wato  hango jini na sauka a qafafun Billy, domin da qarfi ta fizge kanta  daga jikin Hakeem.

Kafin Hakeem yace komai sae ga doctor ya shigo cikin sauri sbd jin hayaniya,doctor yace"subhannallah! Hakeem ya akayi haka ta faru? cikin rud'u Hakeem ke kallon doctor ya rasa me zai ce da shi,doctor ya kalli Billy wacce ke kuka sosai mai tsima zuciya,jini na faman sauka a qafafunta,cikin kuka ta durqusa kan guiwoyinta ba tare da ta damu da jinin da ke fita a jikin ta ba,
 sae maganganu take kan Hakeem ya cuce ta.

Wanda nan Doctor ya fahimci komai,yaje gab da ita yana so ya mata bayani yanda abun yake....tayi saurin sa hannu ta rufe kunnuwanta tace"bana son jin kamoi doctor! bana so!domin naji komai a kunne na kuma naji a jikina da gaske ne abun,domin inajin zafin rad'ad'in abinda ya min!

Tana gama fad'a ta share hawaye da takaici ta nufi hanyar fita daga d'akin kamar wata zautacciya, Hakeem yayi saurin kamo ta,doctor Yace"dora ta kan bed ayi mata allurar bacci"

Da qyar Hakeem ya d'ora ta domin sae fizge fizge take tana kai mai cizo ta koina wanda da qyar doctor ya samu ya mata allura.

A tare suka sauke ajiyar zuciya cike da damuwa.

Nan doctor ya fita sae gashi ya dawo tare da wata baindiya wato likitar da tayiwa Billy aiki,
Nan doctor yaja Hakeem suka fita waje.

 Zaune Hakeem yake amma kwata kwata hankalin sa baya gurin sae halin da Billy take ciki yake tunani..... Wayar sa ce tayi qara koda ya duba Naini ne,maida ta kawai yayi a aljihu domin baya jin zai  iya receiving call a halin da yake ciki,yana ji tana ta faman ruri har ta tsinke.

Docta na fitowa Hakeem ya miqe da hanzarin sa  ta dakatar da shi kan cewa bazai sami shiga yanzu ba domin ana buqatar Billy ta sami hutu sosai.

Jiki sanyaye yaje ya zauna sae dai ya kasa zama ya kasa tsayi har sae da yaje nan wani guri da ake hango mutum ta jikin glass ya leqa inda yaga ancanza mata uniform din jikin ta ancire wad'an da suka 6aci da jini har bedsheets d'inma duk an canza,ya jima yana kallon ta sannan ya koma ya zauna tare da zaro wayar sa ya kira Naini sukayi magana.

Sai gashi ba a wani  jima ba yazo hankali tashe duk yabi ya shiga damuwa.

Da qyar Hakeem ya samu ya kwantar mai da hankali kan cewa ba wani  abu bane.


Sae da ta tashi daga bacci ne aka basu damar shiga wanda a lokacin har Hakeem yaje ya d'auko Mimi daga school.

In banda kuka ba abinda Billy keyi,
 Naini yayi iya qoqarin sa na ganin ta daina kuka tayi magana amma taqi haka ko Mimi,
 bare shi Hakeem da baya ko son yayi magana ta hau shi da masifa kan abinda bai riga ya aikata ba.


Washe gari  aka sallame ta,suka koma gida.

Har akayi kwana biyu Billy bata da aiki sae kuka duk tabi ta rame lokaci d'aya.
   Sosai Hakeem ya shiga damuwa ya rasa ta yanda zai yi ya rarrashi Billy domin ya samu ya fahimtar da ita.

Guraren qarfe biyu na dare Hakeem ya fito daga d'akin shi sbd yaji fitowar Billy,
 yana kallo taje kan two seater ta zauna wacce yaga har yanzu tana cikin qunci sosai,sae faman share hawaye take domin yanzu aikin kenan,kamar daga sama yaji ta fashe da wani  sabon kuka ta hade kai da guiwa.

Sosai kukan ya ratsa jikin Hakeem,ya koma dakinsa cike da damuwa ya d'auko wasu takardu kamar na asibiti.


Ya sauko downstairs gaban Billy ya durqasa kan guiwoyinsa kafin yace komai ta d'ago sbd motsin da taji ta kalli Hakeem da yayi kneel down a gaban ta,sae kawai taga ya kama kunnen sa yace"please am sorry *Pinky*,am so sorry.

*Billy girotruncated by WhatsApp]
[9/22, 6:58 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [8/12/2016] Billy giro😊:

*👛BILLY PINKY DURLING👛*



*Na*
*Billy giro😊*


*Page*
     *👛29&30👛*
Ya sameta taña gyaran tufafin ta da ke cikin wardrobe,
yayi seconds 5 a tsaye yana kallon ta sae yaji wani  irin abu yana qara fizgar shi har dai yanda ya ganta d'aure da towel, ganin kansa kawai yayi rungume da ita, Billy kuwa a firgice ta juya domin ganin wanda ya rungume ta, sbd bata koji shigowar shi dakin ba.
   sosai ta firgita ganin Hakeem kuma gashi ya damqi towel d'inta yana qoqarin raba ta da shi,hannu tasa ta riqe towel d'in gam tana kallon Hakeem da duk ya fita hayyacin sa, tace"Bobby lafiyar ka meye haka?please Bobby stop it"Hakeem kam sae qara matse ta yake a qirjin sa kamar wanda ke shirin mayadda ita cikin jikin shi ga towel d'in ta da yake ta faman ja wanda Billy ta jimqe gam taqi yarda ya raba ta da shi,bakin ta yake qoqarin lalubowa ya had'a da nashi,
 tayi saurin kauda fuskar ta sae kawai taji harshen sa cikin kunnen ta yana yawo da shi cike da qwarewa har wani abu take ji kamar bacci mai dad'i na fizgarta,hakan yasa ta fara jin wani  yanayi a jikin ta wanda bata ta6a samun kanta a ciki ba, nan jikin ta ya fara rawa tana fitar da numfashi slowly slowly kamar yanda take jin harshen Hakeem yana yawo a cikin kunnen ta,kuka ta fashe dashi sbd wata irin matsa da yayi mata Hakeem ya tsaya cak ya daina lasar kunnen ta ba tare da ya sassauta matsar da yayi mata ba.

     Yayi minti biyar matse da ita kafin yake bude idanun sa da sukayi jajir tare da fizge towel d'in ta da qarfi ya jefar,
 Billy ta buga ihu hade da kare qirjinta tana Bobby stop it!

  Hakeem kuwa tunda ya jefar da towel ya tsure gurin da ya jefa towel da ido sbd hango pad da yayi a gurin,
wanda hakan yasa ya fara sassauta riqon da yayi mata nan ya saki jikin ta gabad'aya ya fita daga d'akin kamar wani  zautacce.

  Billy tayi saurin sama d'akin key taje ta fad'a kan bed ruf da ciki tana qoqarin ganin ta saisaita kanta, amma tayi minti ashirin kafin take samu jikin ta ya daina rawa.
  Tashi tayi ta dauko towel d'inta anan taga pad wanda garin gyaran wardrobe ne ya fad'o bata sani ba, dauke shi tayi ta mayar.
  Ta daura towel taje kan bed ta zauna ta dafe kanta da take jin yana mata ciwo yayinda ta shiga tunnin me yake faruwa da Hakeem haka,sae kace wanda ya shiga convulsion,but ai ba haka yanayin convulsion yake ba,amma tabbas da akwai abinda ke damunsa sbd sam ba a hayyacin sa yake ba,ko kuma doctor ne ya bashi maganin da yafi qarfin jininsa,haka ta qaraci saqe saqen ta bata gane komai ba,

  Kallon agogon dakin tayi taga lokacin d'auko Mimi daga school ya kusa gashi tasan Hakeem bazai iya zuwa ba,
 jiki sanyaye ta fad'a toilet.

Bayan ta shirya taje ta d'auko Mimi.


Har dare Billy bata sake ganin Hakeem ba kuma bata nemi sanin halin da yake ciki ba asali ma bata da tabbacin yana gidan ko baya gidan.


 Zaune suke kan dining suna dinner nan Naini ke tambayar Billy,cewa"har yanzu Hakeem jikin ne da bai samu ya fito cin abinci ba?
mimi tace"nima yaya naini tunda na dawo banga yaya Hakeem ba na dauka ko yayi tafiya ne.
   Billy sae jin su take bata ce dasu komai ba.
  Kallon ta kawai naini yayi wanda ya fahimci tunda ya shigo suka suku yake ganin yanayin ta ko magana bata cika son yi ba.
   Nan ya tashi ya nufi d'akin Hakeem yayi ta knocking ba alamar za a bude,
 nan ya bude dakin a hankali ya shiga ya sami Hakeem qundundune cikin blanket sae rawar dari yake,koda Naini yaje kusa da shi yaji jikin sa yayi zafi sosai har blanket din da ya rufa dashi ya d'auka.

 Sosai Naini ya shiga rud'u domin kallo d'aya zakayi Hakeem ka hango mutuwa kusa da shi sbd yanda ya fita hayyacin sa gabad'aya,
Naini bai tsaya wata wata ba ya kira wani  doctor abokin mahaifin sa.

Ba jimawa yazo sae sauri yake sbd akwai inda zaije hakan yasa bai yi wani  qwaqqwaran bincike kan Hakeem ba yace typhoid'fever ke damun shi nan ya rubuta mishi magunguna,yayi mishi
allurai biyu ya wuce.


 Da safe Billy ta fito ita da Mimi suka same shi kwance ya d'an ji sauqi bisa ga jiya, amma duk da haka kallo d'aya zaka yi mishi ka fahimci yana jin jiki sosai.

Naini ne ya shigo da sallamar sa yayi ma Hakeem ya jiki sannan ya ja hannun Mimi domin zuwa kai ta school.
  Bayan sun fita ne ita ma Billy ta juya zata fice sae kuma ta tsaya ba tare da ta juyo ba tace na kawo ma breakfast d'inka yanzu?
 shiru yayi bai ce da ita komai ba domin baya jin buqatar komai face ya kasance da ita, shiyasa ya matsu ta bar gurin domin baya son ya sake samin kansa a cikin yanayin da ya sami kansa jiya wanda shi kadai yasan azabar da yaji na rashin samun ta.

Ganin bai ce da ita komai ba ta wuce.


Yau kusan kwana biyu Hakeem na faman jure azabar da yake ji har ma baya son ganin giftawar Billy,
 shiyasa ma ya fara kulle kansa a daki.
 

Da ya gaji da zaman dakin ne ya fito waje domin ya sha iska,sae ga Mimi tazo ta same shi riqe da ribbon a hannun ta tace"please yaya ka samin didi sallah take koda na fito gurin wanka,shiru Hakeem yayi yana tunanin kenan Billy tayi wanka,
bcs duk a tunanin sa pad d'in da ya gani ranar ya zaci fashin sallah take shiyasa ya barta.
  Nan ya ci gaba da tunanin yau zai kawo qarshen azabar da yake ji kullum ba sassauci,
 kuma fa baya son zubar da ajinsa na nunawa Billy buqatar sa,sae dae kuwa idañ tana cikin bacci zai kusance  tunda ba virgin bace bare in ta farka ta fahimci wani  abu,amma kuma wane irin bacci ne da har zan kusance ta bata farka ba.....kawai ka bata maganin bacci mai qarfi tasha, zuciyar sa ke gaya mishi hakan, yace"ta yaya?... ta hanyar sa mata a abun sha....but a yaya zanyi wannan aikin,
 Wannan karon zuciyar sa bata ce mishi komai ba sae tunani  ya shiga yi da kanshi.... Mimi ce ta katse shi da cewa please yaya,,,sorry Mimi ban iya sa abun nan ba,nan ta koma daga ciki ya ci gaba da tunanin yanda zai yi.


Da dare guraren qarfe 9:00 Mimi ce tazo ta sami Billy ta fito daga wanka ta bata ledar ice cream tare da fad'in yaya yace a kawo miki sannan idan kin gama sha kije ki gyara mishi d'aki.
   Tana gama fad'a ta fita taje suka sha nasu ice cream ita da Hakeem.

Billy kuwa sae da ta shirya sannan tasha nata ice cream ta tashi taje d'akin Hakeem domin gyara mishi.


Tunda ta shiga Hakeem ke faman dubin agogo da yaga tayi minti goma da shiga ya kalli Mimi yace "je ki kwanta kinsan akwai school gobe",
 ba musu ta tashi,
 haka shima yabi sayunta,
Mimi ta shiga d'akin Billy shi kuma ya shiga nashi.

Bai yi mamakin ganin Billy kwance tana bacci kan bed d'insa ba sbd yasan hakan zata faru.

Sae da yaje ya saka key sannan ya rage hasken d'akin amma duk da haka akwai d'an haske.

Kayan jikin sa ya fara cirewa kafin yake hawa kan bed,ya tsure Billy da kallo yana mai jin tsananin baqin cikin kusantar ta da zai yi sbd bai ta6a kawo hakan zata shiga tsakanin sa da ita ba,sae dae kuma ya gwammaci ya kusance ta kan yaje ya aikata zina.

  Yana gama tunanin sa ya cire mata rigar da ke jikin ta ya jefar,ya zamo daga ita sae pant,nan yabi surar jikin ta da kallo cike da ban sha'awa har dai qirjinta da yafi daukar hankalin sa, a hankali ya kai hannu ya zare pant d'in jikin ta tare da rungomota jikin sa ya fara wasa da sassan jikin ta ta koina, musamman qirjinta da yafi maidawa hankali.

*Billy giro😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 7:00 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [ 8/13/2016] Billy giro😊:
*👛BILLY PINKY DURLING👛*



*Na Billy giro😊*


*Page*
     *👛31&32👛*
Haka Hakeem yaci gaba da aikin shi na ganin ya cimma burin shi amma yayi 1hour yana fafutukar cimma burin sa ya kasa,
 kansa ne ya d'aure sosai domin shi dai ba daga gareshi matsalar take ba sae dai ko Pinky da ya kasa samun hanyar shigarta.

Sauka yayi kan bed yaje jikin window yana so ya gano meye matsalar inda ya shiga tunanin ashe mace kan rufe ruf koda kuwa tasha had'uwa da maza.
  Zuciyar sa tace "may be haka ne don haka kaje kayi da gaske ko zaka sami hanyar cimma burinka.

Nan ya koma kan Billy inda yayi mata ta qarfin tsiya wanda yasa ta farka cikin nannauyan baccin da take ta saki qara sosai sau d'auya bata sake ba,haka kuma komai nata bai motsa ba.
 Tatta6a ta ya shiga yi yana d'an girgiza ta amma ba alamar zata sake motsawa,
 ajiyar zuciya ya sauke sbd baya son ta farka ta ganshi tare da ita a cikin wannan yanayi.
   Kayan ta ya dauko yasa mata,shi kuma ya d'auki jallabiya ya saka, ya dauke ta cak ya kaita d'akin ta ya kwantar har da wani  kwantar da teddy kusa da ita ya dora hannun ta kan teddy ya fita daga dakin.


Yaje dakin sa yana ta faman kai komo yayinda yake jin komai ya kunce masa na kasa cimma burin sa da yayi.


Washe gari har lokacin zuwan Mimi school yayi Hakeem bai ji d'uriyar su ba bai kuma ji alamar zasu fito ba.

Hakan yaje yayi ta knocking sae can Mimi ta farka tazo ta bud'e mai.
  Ya shiga d'akin yana mai mamakin ganin Billy yanda ya ajiye ta.
  Kallon Mimi yayi yace yi sauri kiyi wanka lokaci ya qure.

Bayan tayi wanka agurguje ta shirya Hakeem ya dauke ta zuwa school wanda har yaje ya dawo yana tunanin ya kamata ace Billy ta farka haka sbd ruwan allurar da ya tsirga mata a ice cream lokacin gama aikin su  yayi.

Falo yake zaune yana ta kallon agogo har sha biyu bai ji motsin ta ba,
haka kuma naini bai shigo ba sae dai ba Naini ne damuwar sa ba kamar farkawar Billy.


Tashi yayi yaje dakin ta still tana a yanda take,
 6angaren Naini yaje ya same shi sae bacci yake,
 yayi tsaye yana tunanin me ma Naini zai mishi,
 shi da baya son kowa ya sani.
  Amma kuma dole ya kira doctor in yaso yace mai taqi farkawa ne tun baccin jiya.

Hakan ya yanke shawara ya kira doctor ya sanar da shi.

Da yazo suka je har dakin Billy,
   Yana duba ta ya fahimci doguwar suma ce tayi,doctor ya kalli Hakeem yace ai ba bacci take ba doguwar suma ne tayi but garin ya haka ta faru Hakeem?fuska daure yace "Doctor ta ya zan fahimci hakan tana dakin ta ina nawa dakin,
doctor bai ce da Hakeem komai ba sae binciken Billy da ya shiga yi,
can ya nisa tare da fadin ka shirya ta muje asibiti.
   Asibiti doctor? Of course zan yi qwaqqaran bincike ne domin na gano ainihin  abinda ya sumar  da ita.
  Yana gama fad'a ya fita yace kayi sauri ina jiran ka a waje.
  Ba yanda Hakeem ya iya haka ya nemo suturar kirki ya sakawa Billy ya fito dauke da ita suka shiga mota.

Da suka je asibiti cikin 15mnts doctor ya gama binciken sa ya kira Hakeem a office d'insa yace"Pinky ta suma ne a dalilin jin zafin rad'ad'in wani  abu,Hakeem mene wannan abun? Doctor ta yaya zan sani... no kar ka min gardama ka fito ka gaya min gaskiyar mene ne,domin ta haka ne aikin zai min sauqi,
shiru Hakeem yayi yana tunanin ta yanda zai sanar da doctor,har dai da ya tuna cewa yayi masa gardama ba wata sha'awa da ke damunsa to ya zai ce mishi garin kusantar ta ne ta some.
  Doctor ya katse shi da cewa Hakeem daka sanar dani da kar ka sanar da ni zan iya gano koma mene ne but bana son nayi wa matar ka wannan binciken ba tare da naji wani solution daga bakin ka ba sbd wani  dalili, idan kuma kaqi sae na kira Abban ka naji koda akwai wani  ciwo da pinky ke d'auke da shi wanda idan ya motsa ya kan iya sumar da ita.... no doctor kar ka kira Abba bana son suji wannan abun ko kai don ba yanda zanyi ne,, olryt fadi ina jin ka.

 Nan Hakeem ya sanar da shi,wanda ko kad'an doctor bai yi mamaki jin bayanin hakeem ba sbd a nan take ya gano matsalar,kallon Hakeem yayi cike da tausayi domin yasan maganin da ya bawa Hakeem ba zai daina azazzalar sa ba sae idan ya sami mace ko kuma sai idan anyi masa allurar kashe maganin.
  Yace Hakeem matsalar pinky hallita ce wacce ubangiji ke hallito wasu mata da ita wanda koda za'a haife su suna dauke da ita,ma'ana wata tsoka ce da ke toshe gaban mace wacce idan ba a cire mata ita ba d'a namiji ba zai ta6a iya kusantar ta ba,ko mai kuwa qoqarin ganin ya same ta ba zai same ta ba sae dae ya illata ta.
  Kan Hakeem ne ya daure yace doctor nifa bangane ba, abinda nake son ji shine shin dama ita mace idan aka jima ba a kusan ce ta ba ta kanyi wuyar kusanta ne ta rufe ruf?me kake son cewa ne Hakeem ko kana nufin ka ta6a kusantar pinky but ta yaya ka kusance ta bayan tana d'auke da wannan lalurar? No doctor ni ban ta6a kusantar ta ba kawai dai nasan she is not virgin koda na aure ta...ba gaskiya bane Hakeem bcs idan har yanda kamin bayani gaskiya ne kuma abinda nake tunani shine, tabbas ba wani namiji da zai iya kusantar pinky komai jarumta kar sa kuwa dick dinsa ba zai ta6a iya shiga ba bare har ya iya moving,kawai zargin ta kake amma pinky she is virgin,domin ba wata mace da za a ce an ta6a kusantar ta,ta kuma dawo virgin, never,
bare pinky da ke dauke da wannan lalurar, amma tunda kace haka zan sa likitar mata tayi  min bincike akan pinky ni kuma na bincike ka domin a gano wanda keda matsala cikin ku.

Nan Hakeem ya gyad'a wa doctor kai yana cike da tunani kala kala a ransa.

Doctor bai jima ba ya dawo,a nan yayi binciken da zai yi akan  Hakeem inda ya gano ba wata matsala da yake d'auke da ita ma'ana lafiyar sa qalau.

Koda ya gama binciken sa yayi ma Hakeem alurar kashe qarfin wannan maganin ba tare da Hakeem ya nemi sanin ta mece ba kamar yadda doctor bai sanar da shi ba.
 
A nan doctor yace da Hakeem baka da wata matsala Hakeem lafiyar ka qalau bari naje naji result d'in pinky.
 yana gama fad'a ya fita.


Sae gashi ya dawo cikin qanqanin lokaci ya zauna tare da furzadda iskan bakin shi yace"tabbas kuwa wannan abun shine pinky take d'auke da shi wato angurya,
yanzu kasa hannu domin aiki za'ayi mata a cire shi... But doctor kana ganin yi mata aiki ba zai kawo matsala har su Abba su ji ba?no Hakeem ai ba wani  aiki bane bcs ba aikin da idan anyi ace za'ayi dinki bane, kuma idan an cire mata wannan abun she is stiil virgin,
 kuma a cikin sati d'aya zata warke sumul kamar ma ba ayi ba.
   OK doctor but pls bana so idan ta farka taji dalilin da yasa aka yi mata aiki na fiso nayi mata bayani da kaina, nan doctor yace "ba damuwa"
 sannan ya bashi takarda domin yasa hannu.

 Sosai jikin Hakeem  yayi sanyi yayinda yake sa hannu a takarda,Doctor yace
"kar ka sa kanka a damuwa ba abinda zai same ta inshaAllah,

  Hakeem bai ce da shi komai ba bcs ba aikin da za'a yiwa pinky ne ya sashi sanyin jiki ba irin jin cewa virgin ce.


Bayan an  kammala yiwa pinky aiki doctor yaje yaja Hakeem zuwa d'akin da aka kaita.

Hakeem yaje yayi tsaye yana kallon fuskar ta da tayi fayau tayi haske ta qara kyau kamar wata matatta,
 long time Hakeem yana kallon ta sae bacci take,
 yayinda yake jin kansa cikin wani shauqi na daban wanda ya kasa gane cewa son Billy ne.
  Zama yayi kan kujerar da ke kusa da bed d'in da Billy ke kwance, tare da riqo hannun ta yana murza shi a hankali inda ya sami kansa da lumshe idonsa ya dorawa hannun kiss,d'agowar da zai yi ne suka had'a ido da Billy.

*Billy girotruncated by WhatsApp]
[9/22, 7:03 PM] ‪+234 810 038 8117‬: *👛BILLY PINKY DURLING👛*




*Na Billy giro😊*

*Page*
     *👛35&36👛*
Sosai tayi mamaki har dai sunan ta da ya furta abinda bai ta6a yi ba a rayuwar sa,sae dae bata nuna mishi mamakin ta ba sae tashi tayi zata bar gurin yayi saurin riqo hannun ta yace"for God sake ki tsaya ki saurare ni.....ai da kasan Allah da baza ka cuce ni ba,koda yake bazan yi mamaki ba don ka cutar da ni sbd kai maqiyina ne ko maqiyin ma na qarshe domin yanzu na qara tabbatar da hakan ko......Kuka ne ya hana ta qarasa zancen, Hakeem ya tashi tsaye yaja hannun ta suka zauna ya miqa mata takardun asibiti yace"ki duba kiga abinda aka cire miki wanda har yasa kike jin rad'ad'i a gun amma wlh ba kusantar ki nayi ba, sae dae gaskiya nayi niyar aikata hakan amm sae na kasa samunki sbd lalurar da kike d'auke da ita, kuma banyi niyar kusantar ki don haka kawai ba sae don babbar lalurar da nake d'auke da ita wacce ke qoqarin kaini ga aikata zina..... Kaga malam zancen ka ba alamun gaskiya a cikin sa sbd sanin kanka ne nasan zinah ba komai bace a gurin ka,abu ne wanda ka riga ka saba aikatawa.... Pinky ni kuma?....qarya nayi ko kaman ta cewa na ganku da ido kai da Jennifer

Kin gan mu but..... Shiii!that's all.

  Nan ta tashi zata bar gurin ya jawo ta da qarfi har sae da ta fado kan jikin sa tayi saurin tashi tare da fad'in"wai lafiyar ka me kuma kake so ka sake min a rayuwa bayan ka riga ka gama da ni....baza ki bar gurin nan ba har sae kin fahim ce ni domin ni kad'ai nasan yanda nake azabtuwa kan rashin fahimta  ta da kikayi, na rantse miki ni ban kusance ki ba kuma ban ta6a aikata zeenah a rayuta ba!
   Shiru Billy tayi tana kallon Hakeem tace"hm Bobby kai fa namiji ne bazan ta6a yarda da zancen ka ba domin ku ba abin yarda bane,
 don haka ka daina 6ata yawun bakin ka a banza!
   Hakeem yayi shiru ya rasa me zai ce da ita, sae duk yaji haushin kansa sosai har ma yaji ina ma ace bai yi yunquri biyan buqatar sa da ita ba,koda kuwa ace wannan lalurar zata kashe shi ne,a hankali ya saki hannun ta yace"ina so ki min alfarma d'aya ki duba tarkadun asibiti kafin ki bar nan,
Yana gama fad'a ya tashi ya bar gurin,
 ba musu kuwa ta shiga duba takardun wanda a nan ta fahimci komai amma baza ta yarda da hakan ba har sae taje asibiti domin ayi mata binciken da zata fi yarda da hakan.

Nan ta tashi ta koma d'aki.

Washe gari ta fito tayi break fast kamar yadda ta saba.

Bayan Hakeem ya kai Mimi school ya dawo suna kan dining su uku zaune suna break fast,Naini sae yi yake yana kallon Billy wanda tun zaman ta ta fahimci hakan, sae dai ta kàsa gane na mene ne,sbd kallon yayi yawa? Nan dai ta basar.
   Suna gama break fast Naini ya tafi school Hakeem kuwa ya shiga d'akin sa.

 Billy kuwa makullin motar Hakeem ta dauko ta fita zuwa asibiti domin ayi mata binciken da zata fi yarda cewa Hakeem bai kusance ta ba.

Ba yabo ba fallasa ta dawo,amma da alama taji bayanin da take son ji.

Koda ta shigo ta sami Hakeem kwance a falo idanuwan sa a rufe sae dae kamar ba bacci yake ba, tayi tsaye tana kallon shi tace a ranta
_"yanzu zamu d'ora inda muka tsaya sae dae dole na kiyaye duk wani  abu naci ko na sha da zai fito daga hannun ka,domin kare mutuncin kaina"_

Ta wuce haka yace"Pinky"
 ta tsaya cak tana kallon shi yace"meyasa kika kashe wayar ki umma da Abba sunyi ta kira basu same ki ba? ni at all na manta inda na ajiye wyr 3days a go.

 Olryt se kije ki nemi wayar bcs umma na son magana da ke nan ta gyad'a mishi kai ta wuce ya bi ta da kallo cike da so wanda yanzu shi kanshi tabbas yasan ya fara sonta.

Tana shiga d'aki ta cire doguwar rigar da ke jikinta,
ta saka wata riga handless iya qugu da d'an guntun wandon da bai wuce cinyar ta ba.
  Sae da tayi waya da umma kafin take fitowa tazo gab da Hakeem ta zauna fuskar ta na d'auke da shagwa6a,Hakeem sae kallon ta yake yanda tayi kyau sae duk yaji ta qara shiga ran shi yace"me akayi ne pinky?wai ni Bobby yaushe zamu koma ne ka san fa a school anyi resuming har anyi nisa, kar ki damu saura kwanaki kad'an mu koma,ihun murna ta saki had'e da rungumo shi ta bashi peck a kumatu tace gud story Bobby! ta tashi tare da fad'in ina zuwa, Hakeem kam dasqarewa gurin yayi cikin yanayin mamaki yanda tayi hugging d'insa ta kuma bashi kiss sae dae kuma haka Billy take idan ta sami gud story a gun umma ko Abba wanda yanzu ya fahimci rashin umma da Abba ne yasa abubuwan suka fara dawo wa kanshi.


Billy kuwa tana shiga d'aki tace"cab na makara fa, lallai dole na gaggauta nuna ma soyayya ta a cikin en kwanakin nan,na kuma sake da kai sosai tamkar dama can mun saba.

Pringles ta d'auko ta fito.

Da murmushi Hakeem ya tarbe ta domin yana son pringles sosai tashi yayi zaune inda suka fara cin pringles d'in a tare suna kallon TV can Billy ta kalli Hakeem cike da jin bacci tace"Bobby bacci"ok je daki ki kwanta, um um ni anan zanyi bacci"
 ta fad'i haka ne yayinda ta samarwa kanta gurin kwanciya a jikin sa ta hanyar yin pillow da cinyoyin sa ta wani  qudundune qafafunta kamar wata er baby, kallon ta yake inda ya sami kansa da shafar gashin kanta har tayi bacci.

Ta jima sosai tana baccin ta, Hakeem kuwa yana kallo,yana ci gaba da cin pringles ,sae ga Naini ya shigo yana ganin Billy kwance a jikin Hakeem yayi saurin juyawa zai fita, Hakeem yace yadai Naini?yace no ba komai,but ina so zamuyi magana" sae kawai ya fita ya tsaya a bakin qofa,shiru Hakeem yayi shifa ya fara hango wani abu a game da Naini but ko dai kayan da ke jikin Billy ne ya hana shi shigowa,kallon Billy yayi yana tunanin yanda zai yi domin baya son garin tashi ya tashe ta daga bacci gashi da alama baccin na mata d'ad'i sosai,a hankali ya tashi ya d'auke ta cak ya kaita d'akin ta ya kwantar.

Ya dawo yace da Naini shigo muyi magana ba musu ya shigo domin yaga lokacin da Hakeem ya maida Billy d'aki sae duk quncin da yake ciki ya qaru.
  Ya sami guri ya zauna yace dama ba wani  abu bane ina so zan koma hostel da zama,meyasa naini?shiru Naini yayi domin shidai abinda ya sani ko kad'an baya son ganin jikin Billy na haduwa da na Hakeem,
se can yace"sbd zamu fara exam...but Naini ai duk d'aya ne bcs nan ba mai takura ka, I know but kawai dai nafi son can, Naini ko dai wani  abu aka ma wanda bai ma ba ka fad'a min sae mu gyara kaji,ba abinda kuka min kawai dai ina son na tafi can domin ganin nake kamar zan fi karatu a can,olryt but please kar ka tafi yanzu ka bari idan pinky ta tashi daga bacci,
 ba musu yace shikenan zan koma school dama abu nazo d'auka.



Guraren qarfe biyar Hakeem ya shigo gidan  ya dawo daga dauko Mimi,Billy wacce ta bude musu gate,ta qarasa da gudu ta tarbo Mimi taje ta riqo hannun Hakeem cike da shagwa6a tana d'an shillo dashi a hankali,ta wani turo baki tana kallon shi tace"shine kaje d'auko Mimi baka je dani ba,bayan da safe kasan bada ni aka kaita school ba,, am sorry kinji na jima da fita domin koda na fita duk kina bacci ban kuma dawo ba sae yanzu...maqale kafad'a tayi tace"um um ni bazan haqura ba sae an fita dani domin na jima ban fita ba, cike da murmushi Hakeem ya lakuta hancinta yace"kin manta yau da safe kin fita"to ai wannan ba yawo bane.. Olryt naji amma yau nagaji da yawa sae dai gobe,
ya fad'i haka ne yayinda suka shigo falo,ta saki hannun Hakeem,
 ta tafi da sauri gurin Naini sbd dama game ce suke bugawa taji odar Hakeem.

Hakeem yayi tsaye yana kallon ta yace da Mimi wacce ke qoqarin zuwa gurin su"no mimi je kiyi wanka kizo kici abinci ba musu ta wuce ya kalli Billy da har ta fara sake ihun murna yace"pinky je kiyi ma Mimi wanka"oh oh Bobby ba kace taje tayi ba,
 kallon ta kawai yayi bai ce mata komai ba ya bar gurin, da sauri ta tashi tabi bayan shi, Naini kuwa ya bita da kallo har suka shiga d'akin Hakeem,suna shiga tace wai Hakeem meye haka kasan fa Naini baya jin dad'in abinda kake yi may be ma akan shi ne yace zai koma hostel sae da na lalla6a shi ne yace ya fasa komawa kuma yanzu kazo..... maganar Naini ta ishe ni haka fa!
Ta kalle shi cikin fushi ta fita daga dakin.
  Hakeem ya bi ta da ido shi ba abinda ke 6ata mai rai irin qananin kayan da take zama da su a gaban Naini.

 Tun lokacin Billy fushi take da Hakeem har sukayi dinner.

Bayan tayi shirin kwanciya sae ga Mimi tazo tace"didi yaya Hakeem yace kije yana kira"yana a ina? yana a falo,
 ba tace komai ba tayi kwanciyar ta tana chat,
 sae can ta tashi taje  falo bata same shi ba taje d'akin shi ta samu yana toilet zata fita kenan ya fito tayi saurin juya bayan ta shaye da toka,Hakeem Yazo gab da ita ya rungumota ta baya,tayi saurin kame jikinta tace"Bobby ka saka towel d'in mana, ai akwai towel a jikina.... a wuyan ka ba,pls ka saka shi inda ya dace ,gaban ta ya dawo tayi saurin rufe idon ta tace "ah ah Bobby bakada kunya ko zan fita fa"
 bud'e idon ki kiga Allah da towel a jiki na,
 a hankali ta bud'e idonta,taga kuwa yana d'aure da towel a qugunsa sae kuma d'an qarama da ke kan wuyansa tace"uhm ashe da gaske kake na zaci ka fito a yanda ka saba,
Shiru yayi domin tabbas yayi niyar fitowa a yanda ya saba sae dai jin shigowar ta ya hana hakan can yace"amma ya akayi kika san yanda nake fitowa wanka?

 Hannu ta kai taja kumatun sa duka biyu tace"bayan ganin farko da na ma sae gashi ranar na shigo zan gyara ma d'aki,
 naga ka fito daga wanka sae kayi sauri ka koma sae nayi kaman ban ganka ba nayi ma wayon manya"
 ta fad'i haka ne had'e da yi mishi gwalo, murmushi yayi tare da jawo ta jikin sa,,
da wasa ya riqi d'an sirin hannun rigar ta yayi kamar zai zare hannun daga jikin ta yace"ai kuwa sae na rama yanzun"Billy tayi shan tokar en yara tare da buge mishi hannu tace"ni ka daina ta6a ni ka manta fushi nake da kai"
to ai ke kika fara ta6a ni, cike da kunya ta cusa fuskarta a qirjin sa tana dariya ciki ciki sbd yanda yayi magana kamar wani yaron goye, nan Hakeem ya shiga yi mata cakulkuli yace"ai sae kin fitar da dariyar ta fito, dariya ta shiga yi sosai tana fadin ka daina mana,bai daina ba sae zille zille take har suka je kan bed Hakeem yayi mata rumfa yana ci gaba da mata cakulkuli can ya dakata ya kai hannu a hankali yana share mata en guntayen hawayen da suka fito mata kan dariya,kallon shi ta shiga yi long time sae kawai ta tuna da qawar ta Feenah a lokacin take sanar da ita cewa
*"Bobby baya da matsala ta koina matsalar sa d'aya ita ce qiyayyar da yake nuna miki*.

*Billy giro😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 7:14 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [8/18/2016]
 *👛BILLY PINKY DURLING👛*




*Na Billy giro😊*



*page*
    *👛39 to 41👛*
Dasqarewa Billy tayi komai nata ya kasa motsi sae hawaye da ke faman zarya a kumatun ta, qoqarin sulalewa take ta fadi Hakeem yayi saurin tarbo ta ta fad'a jikin sa, tace"na shiga uku Bobby na kashe Nai....saurin rufe mata baki yayi ya girgiza mata kai yayinda idanuwan sa suka ciko tap da qwallah yace"nine na kashe Naini,
 ni na kashe shi da hannu na kar ki sake yunqurin d'orawa kanki.
  Tsananin mamaki ne ya bayyana a fuskar ta tace"ya zaka ce haka Bobby bayan ba kasan yanda abin ya faru ba,wlh Allah nice....shiii! na sani amma ki barshi a yanda nace,why Bobby....police suka gani kai tsaye sun zagaye su,duk Billy tabi ta qara rikice wa kamar yadda shima Hakeem ya shiga rud'u domin bai san ya akayi en sanda suka sani ba har suka biyo su asibiti.... Doctor ya dafa Hakeem yace Hakeem nine na kira su domin bansan daya daga cikin Ku ne yayi kisan ba,sbd kayi min bayani a rikice inda ka nuna min kamar wani  ne ya aikata aikin shiyasa nayi gaggawar kiran police,amma don Allah kayi haquri wlh...
no doctor ko baka Kira su ba nayi niyar hakan sbd kisan mutum ba abune da za'a iya rufe shi ba,bare mahaifin Naini mutum ne mai tsananin bincike akan komai, shiyasa ya zama dole tun wuri na miqa kai na ga hukuma.

 Nan ya miqa kanshi ga police suka sa mishi handcuff,kuka Billy ta fashe dashi tana kallon doctor tace"doctor wlh ba shi yayi kisan ba nice,don Allah kar ka bari aje da shi"
      Hakeem yace"pinky banyi haka don komai ba sae don fitar da ke daga qunci,sbd haka ki daina kuka kinji domin zan iya jure komai indai akan ki ne.

    Yana kawo nan police suka jashi, Da gudu Billy ke binsu cikin kuka sae kuma ta tsaya cak"inda ta
shiga magana a cikin ranta
_"meyasa zan damu da yawa haka bayan ba son Bobby ko d'as a cikin zuciya ta da har zanji tausayin shi,kuma hakan da yayi tamkar ya samar min wata dama ce da zan ku6uta da auren sa har abada....._
  No ba haka naso ya faru da kai ba Bobby ko don hallacin da kamin a yanzu,,ni dai  kawai fatana na rabu da qaddararren auren ka shi kawai nake buqata a rayuwa ba mutuwar ka ba.
   Tayi maganar ne a fili kuma cikin kuka kafin take durqushewa gurin tana ci gaba da kuka tana kallon su Bobby da sukayi nisa har suka 6ace mata shima kallon ta yake.
   Mimi ce tazo ta fada  jikin ta ita ma kukan take sosai.
  Cike da tausayi doctor yazo yana lallashin su,tace doctor don Allah ka fitar da Bobby wlh Allah bana so ya mutu.
  Doctor bai ce da ita komai ba,domin ya shiga mamakin zancenta da yaji yanzu ace duk hallacin nan da Bobby yayi mata tana kan bakar ta na ganin auren su ya rabu,nan dai ya basar da zancen ya ci gaba da lallashin su.

Wanda da qyar ya samu ya lallashe ta ya maida su gida.
 

Haka suka kwana cikin kuka,
 Mimi ce kadai ta samu bacci ya d'auke ta Billy kuwa tunda suka dawo take faman kiran number umma da Abba amma ta kowannen su taqi shiga.
      Tashi tayi ta d'oro arwala,tayi ta nafilfili tana roqon Allah kan ya taimake ta yayi gaggawar fitar da Hakeem.
  Daga qarshe ta hade kai da guiwa tana ta rusar kuka inda ta sami kanta da jin wannan hallaci da Hakeem yayi mata,da ace Allah zai ku6utar da shi da kuwa tayi rayuwar zaman aure da shi har abada duk da kuwa ko kadan bata jin son Hakeem a cikin ranta.

Washe gari tunda safe taji door bell da sauri ta fito har tana had'awa da gudu ta bud'e qofar tare da fad'in "Bobby".
  Tana ganin doctor ne kuka kawai ta fashe da shi,cikin dasasshiyar muryar ta da tasha kuka tace"doctor tun jiya bana samun wayar su Abba don Allah ka fitar da Bobby,nasan zasu baka shi tunda ba d'an qasar su ya kashe ba, pinky ko ba d'an qasar su ya kashe ba zasu hukunta shi a bisa kisan kai da yayi cikin qasar su kafin suke miqa shi ga hukumar qasar mu.... Haba doctor don Allah ka taimaka mana, nidai ko yaya ne ka fitar da shi please doctor,
 ta fadi haka ne yayinda ta durqusa kan guiwoyin ta tana kuka mai ban tausayi.
   Da sauri doctor ya bar gurin yaje cikin motar sa ya zauna hade da jinginawa cike da damuwa,yace "sae dai kiyi haquri pinky domin ba yanzu ne ya dace na bayyana cewa Naini yana raye ba,bare har na fito dà Hakeem har sae na fahimci ra'ayin ki ya canza gabad'aya kema kin fara son Hakeem kamar yadda ya fara sonki.


𦰊 D'agowar da zai yi ne ya hango pinky ta jikin mirror ta wuce cikin sauri nan ya fahimci tabbas pinky taji zancen sa, idan kuwa haka ne ta 6ata mai tsari.
 
Cikin rashin jin dadi ya fito mota ya shiga cikin gidan rai 6ace Billy ta kalle shi taja hannun mimi suka haura sama,tana tunanin lallai doctor nan ya akayi har yasan ba da gaske take son Hakeem ba.

Shi kuma doctor ba yanda ya iya domin ya fahimci ta ji sak me yace.
   Nan ya fita bai dawo ba sae tare da Hakeem,wanda tun cikin mota yake tambayar doctor ya akayi ne.
  Bai ce da shi komai ba sae tunanin abinda zai ce da shi yake bcs baya son yasan tun farko Naini bai mutu ba,sbd shi kad'ai yake tsarin shi na ganin ya daidaita tsakanin su kafin su koma Nigeria.

Sae da suka fito cikin mota sannan yace"ina taya ka murna sosai Hakeem bcs doguwar suma ce Naini yayi yau da safe ya farfado wanda hakan yasa nayi matuqar farin ciki marar misaltuwa.
   Cike da tsananin murna Hakeem ke kallon doctor yace to ai doctor gurin shi ya kama ta ka fara kaini tukun, a'a gabadayan ku nake son muje don haka kaje ka fito da su pinky.


Duk maganar nan da suke pinky na hango su ta jikin window sae duk ta d'auka da hadin bakin Hakeem ciki,inda ta shiga tunanin kenan Hakeem ba soyayyar gaskiya yake mata ba ko hallacin da yayi mata don kawai ta so shi ne yayi, wato kenan shine ya gano plan d'inta ya sanar da doctor shine  suke son plan d'in ya koma kanta,to me ya kamata nayi yanzu?
  Tana cikin haka ne taji alamar zai shigo da sauri ta haura sama ta shiga d'aki.
 
Cike da murna Hakeem ya shiga d'akin ta ya same ta ruf da ciki kamar mai bacci"yace bacci kike pinky ki tashi gani na dawo bcs naini is alive, shiru tayi tana sauraren shi da mamaki wato doctor bai fahimci taji ba kenan lallai zata nuna bata ji ba,in yaso taci gaba da bin su har taga iya gudun ruwan su.

Tashi tayi tana kallon Hakeem cike da murna tace"da gaske Bobby da gaske Naini yana raye!?cike da murmushi ya gyad'a mata kai yace "ashe ba mutuwa yayi ba doguwar suma ce.... ihu ta saki ta qanqame shi sae kuma ta fashe da kuka tace"inace basu ma komai ba ko?ba abinda suka min,nan ta share hawayen ta yace ina Mimi? wanka take,kefa kinyi wanka domin yanzu asibiti xa muje gurin Naini, Bobby ta ya zan ji qarfin wanka bayan kana cikin wani  hali,olryt ba gani na dawo ba ai sae kije kiyi wanka yanzu, maqale kafada tayi tare da qara mannewa a qirjin sa tace"ni sae na gama ganin ka tukun,cike da jin dadi yake kallon ta sae ga Mimi ta fito daga wanka, yace"kinga Mimi ta fito je kiyi wanka nima zanje nayi amma kiyi sauri domin doctor yana jiran mu fa.
  Nan ta tashi ta fad'a toilet  shi kuma ya fita.
   Mimi cike da murna take shiri domin kafin Hakeem ya fita ya sanar da ita komai.


Tsaye yake jikin mirror ya fito daga wanka har ya saka tufafi yana sanya buttons d'in rigar shi sae ga Billy ta shigo cikin shiri,
 taje a hankali ta rungumo shi ta baya inda suke hango juna ta jikin mirror, a hankali ya sauke ajiyar zuciya domin qamshin turaren Billy da ya shiga hancin sa tace"nayi ma wayo na riga ka fitowa har na shirya kai sae yanzu kake shiri,,uhm ai don ba kya kwalliya ne kika riga ni,,au to kai kana yin kwalliyar ne? eh mana baki ga kullum se kyau nake qarawa kamar mace,murmushi tayi yayinda take qarewa fuskar shi kallo ta jikin mirror tace"haka ne fa amma ba wata kwalliya a fuskar ka,kuma fuskar ka ba kyau sae muni kamar tawa,
 saurin kallon ta yayi ya girgiza kansa kawai domin shidai yanzu baya ganin munin ta ta koina da ne kawai. yace"ke muni ne dake?eh mana ji hanci na kamar zai ta6o bakina, ga d'an qaramin baki kamar wacce aka emma, idanu kamar wata mai jin bacci,yace"kenan baki gode Allah ba, ya fadi haka ne yayinda ya juyo yana kallon ta,tace"a'a wlh na gode Allah fiye ma da yanda kake tunani,to meyasa kika ce haka? Sbd kawai naji dad'in bakina amma da wasa nake.

Nan yaja hannun ta suka zauna kan bed yace"ina so naji shin me ya had'a ki da Naini har hakan ta faru"shiru tayi tana kallon shi kafin take sanar da shi yanda abin ya faru.
   Kansa ne ya d'aure sosai yace"pinky ko dai akwai wani  abu tsakanin ki da naini kike 6oye min?a'a wlh,to Ko kun sami sa6ani ne? ko d'aya, ok zo muje nama ji kamar Mimi na kiran ki.
   Nan suka fita suka tarar da doctor cikin mota.

 Tafiya suke yayinda doctor ke hango Billy ta jikin mirror ta wani  narke a jikin Hakeem sae labari suke bawa junan su suna dariya,hakan yasa ya d'anyi mamaki  yaushe hakan ta fara faruwa tsakanin Bobby da Billy domin duk a tunanin sa ko kusa da Hakeem bata zama bare zancen had'a jiki,nan ya kawad da zancen sbd sun iso asibiti.

Koda suka shiga sun sami Naini idanuwan sa a lumshe sallamar su ne yasa shi bude ido inda ya sauke su kan Billy wacce ke riqe da hannun Mimi.

  Doctor ne ya taimaka mishi ya tashi zaune wanda har yanzu idon shi na kan pinky kafin yake kallon Hakeem yace"am sorry to say Bobby and u  pinky i am really sorry, i dnt mean to hurt u, ni kaina ban san meyasa nayi yunqurin aikata abinda nayi niyya ba kawai dai na tsinci kaina da tashi aikata hakan sbd son da nake miki.... saurin kallon shi tayi yace"of course ina sonki pinky ina sonki sosai, tun muna yara bani da burin kasancewa da kowa face ke, ban ta6a tunanin zan rasaki ba pinky, shiyasa ban furta soyayya ta a gare ki ba,
wanda nayi hakan ne har sae idan mun kammala school nida ke ko zan sanar da ke sae gashi kai tsaye naji auren ki wanda ya ritikita min tunani gabad'aya amma idan na tuna wanda aka had'a ki aure da shi sae naji kamar nan kusa zan same ki matsayin mata sbd sanin cewa ba kwa son junan ku ko kad'an,
 sae dai zaman da nayi daku ya fahimtar dani wani abu wanda na fara cire ran zan same ki a matsayin mata, shine zuciya ta tayi  ta ingiza ni kan na d'auke ki naje dake can inda zamuyi rayuwar mu mu kad'ai gurin da ba wani d'a namji da zai kalle ki bare har naji zafi a raina,amma kiyi haquri da kuskuren da nayi sharrin so ne da kuma sharrin shaid'an.

Pinky a yanzu bani da wani buri a rayuwa da ya wuce na sami mace mai irin hallayar ki da ma komai naki domin idan ban sami haka ba bana jin zan ji dad'in rayuwar duniya har na koma ga mahallici na.....kar ka ce haka Naini ka tuna fa Allahn da yayi ka shiya d'ora maka sona kuma kai tsaye zai iya yaye maka sona ya kuma baka mace wacce ta fini da komai kuma ka daina cire ran ka rasa ni ba mamaki watarana zan zamo taka.
   Tayi maganar ne cikin muryar kuka sbd sosai Naini ya bata tausayi domin duk a cikin kuka yayi zancen shi.
   Hakeem kam duk kishi ya rufe mishi ido shiyasa ko kad'an bai ji tausayin Naini ba sae ma haushin sa da ya ji.
 
  Da dare bayan sun koma gida pinky ta fito daga wanka tayi shirin kwanciya cikin rigar ta pink iya guiwa.
   D'akin Hakeem ta nufa sbd tun a asibiti ta fahimci fishi yake da ita.
 
Tana shiga ta same shi riqe da glass cup zai sha ruwa yana ganin ta ya fasa shan ruwan.
 kafin ta qaraso ya isa gurin ta fuskar shi a daure Yace"lafiya me ya kawo ki d'aki na?kallon shi tayi sau d'aya ta kauda kai ta rasa meyasa take jin ba dad'i sbd fishin da Hakeem keyi da ita,duk da kuwa tana ganin kamar plan ne bada gaske yake kishin ta ba.

Magana nake miki kin min shiru!idanuwan ta ne suka ciko tap da qwallah tace"Bobby meyasa kake fushi dani?in dai akan Naini ne sanin kanka ne mutum baya d'orawa kanshi so.... Naji mutum baya d'orawa kanshi so domin naga hakan a tattare dani amma meyasa kika kama mishi kuna ta kuka har kina ce mishi kar ya cire ran wata ran zaki zamo tashi...ai gaskiya na fada Bobby sbd ba wanda yasan gobe....nasan da hakan ba sae kin sanar da ni ba, amma ke ba don haka kika gaya masa cewa wata ran zai same ki ba ki gaya min meyasa kika ce masa haka?.....sbd na fahimci yana sona sosai shiyasa nake son kwantar mai da hank....kafin ta qarasa zancen ta se kawai taji qarar fashewar glass cup d'in da ke hannun shi, ya kuma jefo shi kusa da ita har sae da tayi saurin matsawa.

A tsorace ta
fashe da kuka tana kallon hannun shi da ke fitar da jini, shima Hakeem kallon ta yake cike da nadamar jefo mata cup,cikin muryar lallashi yace"pinky na same ki ne?girgiza mai kai tayi yayinda ya ware hannyensa alamar tazo,
 da sauri taje ta shige jikin sa tana kuka sosai sae haquri take bashi,,,is ok pinky amma don Allah kar ki sake furta cewa wani  yana sonki a gabana kinji.
    gyada mishi kai tayi hade da share hawayen ta taje ta dauko first aid kit taja hannun shi ta zaunar da shi kan bed,a hankali take cire mishi glass d'in da ya soke mishi hannu wanda har ta gama treatment din shi kallon ta yake,d'ayan hannun sa ya kai yana share mata hawaye domin har lokacin kuka take.
   Nan ya matsa gab da ita ya lumshe idon shi yayinda ya kai lips dinsa a hankali kan nata ya zira harshen sa wanda yayi 3mnt kafin yake zarewa, ba yabo ba fallasa pinky ke kallon shi ta kwanta a hankali kan qirjin sa tare da sauke ajiyar zuciya,shiru sukayi na d'an wani  lokaci d'akin yayi tsit kamar ba kowa Hakeem sae shafar sumar kanta yake, can ya katse shirun da cewa ki fara shiri domin gobe ne kad'ai muke cikin qasar nan.

*Billy giro😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 7:18 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [8/20/2016] Billy giro😊:
 *👛BILLY PINKY DURLING👛*


*Na Billy giro😊*



*Page*
   *👛42 to 44👛*
Ba tare da ta d'ago ba tace"su umma zasu dawo ne gobe? tana nufin iyayen su Naini.
  Yace "inshaAllah"
tace "Allah ya kawo su lafiya yace"Amin"
 Daga haka sukayi shiru.
  Yayinda Billy ta qara narkewa a jikin sa kamar mai jin bacci,ba wai don tana jin baccin ba sae don yau taji dad'in kwanciya a jikin shi sosai  fiye da kullum,
 koda yake kullum duk ta6a jikin sa da take bata ta6a jin wani  abu makamancin haka ba sae yau wanda har ma ji take tamkar su tabbata maqale da juna don kar ta daina jin dad'in da take ji a yanzu.

 Shi kuwa Hakeem a matse yake gurin domin har zufa ya fara sae Allah Allah yake ta tashi domin shi kad'ai yasan azabtuwar da yake dama kullum ta6a ta da yake yana yi ne sbd idan bai ta6a jikin ta ba har wani zazza6i yake ji idan kuma suka jima a maqale shi kad'ai yasan azabtuwar da yake amma hakan yake jurewa kullum.
   Duk da kuwa ba ita ce macen farko da ya fara ta6i ba amma a kanta kad'ai ya fara jin hakan.
   A hankali yake d'aga ta kan qirjin sa, ta kalli yanda ya matse qafafun sa kamar mai jin fitsari tace"Bobby zaka je toilet ne?da qyar yace"no pinky tashi kije daki kiyi bacci kinji, bcs bacci nake ji sosai, ba musu ta tashi kan jikin sa ba don taso ba domin da bai ce komai ba sae dai ta lafe kan jikin sa har safe.

A daren ranar kowannen su sae juyi yake da qyar suka samu bacci ya d'auke su.

Washe gari ta fito daga wanka kenan tayi kici6is da Hakeem ya shigo d'akin,
saurin kauda idon shi yayi domin daurin towel d'in ta kamar wanda ke shirin sa6ulewa a qirjin ta ba wani  daurin kirki take yiwa towel ba sae duk tabar rabin mama a waje kamar d'aurin en boarding school,sae duk yaji sh'awar ta sosai har dai yanda yaga d'igo d'igon ruwa a jikin ta.
   Sae da ta gyara d'aurin towel d'in sannan ya iya kallon ta yace"yau da wuri zaki had'a break fast sbd da wuri su umma zasu dawo.
   Yana gama fad'a yasa qafa zai fita tace"Bobby"ya juyo a hankali yana kallon ta, tazo gab da shi ta riqo hannun sa da ya jiwa ciwo jiya,cike da damuwa har tana ji kamar tayi kuka sbd ganin yanda hannun ya kumbura sosai,nan taja shi suka zauna kan bed, sannu a hankali take walwale mishi bandage har ta cire taje ta d'auko first aid kit,a hankali take wanke mishi gurin da kad'a da sprit.
 bayan ta gama ta sa mishi wani  sabon bandage.
   A natse ta d'ago tana kallon shi taga ashe ita yake kallo tace"sannu ko?ya lumshe idon shi tare da fad'in kema sannu,ba tace da shi komai ba domin ganin take taci ya mata sannun sbd ita kad'ai tasan zafin da taji a lokacin da take wanke  mishi gurin sae taji abun har cikin ranta tamkar ita ke dauke da jin ciwon.
    Nan ya tashi ya fita ita kuma taje ta shirya sannan ta fito zuwa kitchen ta sami Mimi da Hakeem zaune a falo mimi na biya karatun qur'ani.


Sae da ta gama had'a break fast ta jera abun da duk za'a buqata kan dining.

Suka ji oda da gudu pinky taje ta bude gate cikin murna.
   Koda suka fito cikin mota har su Hakeem sun fito,
 Mimi taje da gudu ta fad'a jikin umman ta kafin take zuwa gurin Abban ta.
   Haka Billy da Hakeem suka je suka tarbe su sannan suka shiga daga ciki.
 Bayan sun gama cin abinci ne suka je asibiti domin Hakeem ya sanar da su tun kafin su dawo.



Da dare guraren qarfe goma da rabi Hakeem ne kwance sai juyi yake kan bed baya da muradi irin yaji pinky kwance a qirjin sa har ma jin yake kamar ya kira ta a waya tazo ta taya shi bacci tunda Mimi bata nan.

Yana cikin haka ne yaji knocking da hanzarin sa ya tashi ya bude dakin.
 pinky ya gani rungume da qatuwar teddyn ta,ajiyar zuciya ya sauke a hankali sannan ya bata hanya a natse ta shiga daga ciki,tayi tsaye ba tare da ta nemi guri ta zauna ba,yaje gab da ita har suna jin qamshin turaren juna yace"ya baki zauna ba ko wani  abu kike so? shiru tayi tana kallon shi domin ita kanta bata san me ya kawo ta dakin ba, kuma gashi a daki ta kasa bacci sae faman juyi take wanda duk ta juya ba abin da ke fad'o mata a rai sae Hakeem.... Ki min magana kinji pinky,
still kallon shi take yayinda hawaye suka ciko tap a idon ta har suna qoqarin zubowa, da sauri Hakeem ya dafa kafàdar ta yace"pinky mene ne gaya min kinji"sautin kukan ta ne ya fara fitowa yayinda ya kar6i teddy ya ajiye.
    A hankali ta fad'a kan jikinsa yayinda sautin kukan ta ke qara fitowa,duk Hakeem yabi ya damu sosai sae tambayar ta yake lafiya?cikin kuka ta d'ago tana kallon shi tace"uhm uhm nima ban sani ba"no pinky kodai wani  abu aka miki, gaya  min waya ta6a ki? ya nuna kanshi da yatsa yace "nine?girgiza mai kai tayi yace"ko Abba? umma fa?abokannan ki? duk girgiza mai kai tayi tare da fad'in nifa ba abinda aka min,
bai ce da ita komai ba sae jan hannun ta yayi suka zauna kan bed yakai  hannu ya shafo cikin ta da ya lafe sosai yace"kina jin yunwa?gyad'a mishi kai tayi,ya tashi ya dauko fresh milk da cup ya tsiyaye yaje yana bata har sae da tace ya ishe ta sannan ya bata ruwa tasha ya  zaro tissue ya goge mata d'an qaramin bakin ta yace"ki daina zama da yunwa kinji bcs bana so"gyada mishi kai tayi  sae kawai ya dauke ta cak ya kwantar da ita ya rufa mata blanket yaje ya kwanta tare da rage hasken d'akin.


Har guraren 11:30 bacci ya kasa d'aukar su kowa nason yaji d'an uwan sa manne dashi.
   Hakeem ne ya kasa haquri ya juyo ya kalli Billy yace"meyasa kin kasa bacci tun d'azu ko so kike ki koma d'akin ki?saurin girgiza mai kai tayi tare da fad'in tsoro nake ji Bobby"abu ga mai jira da sauri ya matsa gab da ita tare da rungume ta yace"yi baccin ki haka ba abinda zai same ki kinji"bata ce komai ba sae qara shigewa tayi a jikin sa shi kuma yana faman bubbuga bayan ta kamar wata er baby wai so yake tayi bacci,
 daga haka ya fara shafar bayan ta sannu sannu har ya soma zuwa koina na jikin ta,duk pinky naji ta fara jin wani  iri amma ta kasa hana shi,duk da kuwa taji yanda ya rikice har yana qoqarin raba ta da rigar jikin ta, bai cire mata rigar ba sae hannun sa taji kan qirjin ta yana wasa da dukiyar fulanin ta son ransa,
 nan jikin ta ya d'auki rawa duk tabi ta tsorace muryar ta na rawa tace"Bobby....saurin d'ora yatsan sa yayi a bakin ta yace "Shiiii!pinky wasan yana min dad'i sosai pls kar ki katse ni"
 nan ya had'e bakin su gam yana tsutsar lips d'in ta kamar wanda ya sami alawa,nan ya samu cikin hikima ya raba ta da rigar jikin ta ya bar ta da d'an pant haka shima boxer kadai ya bari a jikin sa,kuka ta ajiye mishi sbd yanda ya haukace yana shan mamman ta, cak ya tsaya domin jin kukan ta yake tamkar ana hura mai wani  zafin bala'i cikin kunne.
    Rungume ta yayi sosai a qirjin sa yana fitar da wahalallen numfashi yakai  bakin sa gab da kunnen ta yace"pinky zan mutu please kimin abu d'aya ko zan iya bacci"muryar ta na rawa tace me zan maka Bobby? nan ya gaya mata abinda zata mishi wanda take ganin kamar yafi qarfin ta amma tsabar tausayi yasa ta mishi inda cikin 15mnt yaji sauqin komai sai qara rungume ta yayi a jikin sa suka shiga bacci.

 Koda ya farka da Asuba bai ga pinky ba but bai yi mamaki ba domin ya tuna lokacin da yaji ta zare jikin ta daga nashi.
  Tashi yayi yaje yayi arwala yayi sallah yaje ya murd'a qofar pinky yaji ta gam nan ya koma d'akin sa domin baya so ya tashe ta.
   Pinky kuwa tana jin lokacin da Hakeem ya maurd'a qofa amma ta share shi ba don taso ba sae don ta hana zuciyar ta abinda take ji game da Hakeem wacce tun lokacin da ta sato jiki ta dawo d'aki sae haushin kanta take ji kan ta kai kanta d'akin Hakeem ta sake mishi jiki ya ta6a ta duk inda yaso abinda mai son ta da gaske kad'ai ya kamata ta bawa wannan damar ba Hakeem ba da take ganin son plan ne yake mata.
   Kuka ta fashe dashi sosai tana tambayar kanta meyasa ta fara son Hakeem a lokacin da ta fahimci ba da gaske yake son ta ba❓.
     Bata da amsa nan taci kuka har ta gode Allah tana cikin kukan ne taji Hakeem na mata knocking da sauri ta share hawayen ta taje ta bude qofa kad'an bcs bata son ya ganta kar ya fahimci kuka take.
 Yace "je kiyi wanka time zai tafi kinsan a 12am zamuyi tafiyar" gyad'a mishi kai tayi tare da rufe qofar bata d'aga gurin ba sae manna bayan ta tayi jikin qofa tana kuka marar sauti nan ta zame jiki ta zauna qasa ta hade kai da guiwa tana ci gaba da kuka sbd tuna mata tafiyar tamkar ya tuna mata zasu rabu sbd bata jin zata barshi ya aiwatar da plan d'in shi kafin ita.
     Da qyar ta hana kanta kuka ta fad'a toilet tayi wanka tana gama shiri taji knocking taje ta bude ta sami Hakeem a tsaye cike da kulawa ya riqo hannun ta yace"zo muje kiyi break fast.
 
Tafiya suke kan staircase sae kallon shi take inda ta fahimci fuskar nan tashi d'auke take da farin ciki fal.

Suna zuwa kan dining ya zauna tare da d'ora ta kan cinyar shi ya bude kula soyayen dankalin turawa ne da soyayyen qwai se plantain sunyi kyau sosai,
 kallon shi tayi da mamaki tace"Bobby kuku ya dawo ne? A'a nine kukun mu na yau, kallon shi ta shiga yi domin tasan Hakeem bai iya komai ba,idon ta ya kai kan hannun sa inda taga ruwan mai ya qona shi har da yankan wuqa, kamar zata yi kuka tace"Bobby jibi yanda ruwan mai ya qona ka kuma har da yankan wuqa"forget about it, me yake damunki naga idon ki har ya soma kumbura kamar wacce tayi kuka"
 ya fad'i hakane yayinda yake qarewa fuskarta kallo,duqar da kanta tayi tare da fad'in bacci ne"a u sure? gyada mishi kai tayi,nan ya sauke ajiyar zuciya ya fara ciyadda ita a hankali, kar6ar abincin take cike da damuwa bcs sae kallon hannun sa take da ya qone.
   Yana cikin ciyadda ita ne ta kai hannu zata qarasa shigar da arish d'inda bai kammala shiga bakin ta ba, Hakeem yayi saurin dakatar da ita yace "kar ki 6ata hannun ki"
  Shi ya shigar da arish d'in a hankali cikin bakin ta,Billy sae kallon shi take kamar mai neman wani  abu a fuskar shi yace"me yake faruwa ne pinky ko wani  abu kike so? girgiza mishi kai tayi tana qoqarin tashi kan jikin sa tace"na qoshi".
    Sallamar doctor suka ji Hakeem ya amsa sallamar yayinda ya bawa Billy ruwa tasha ya zaro tissue ya goge mata bakin ta.
  Gaban ta ne ya fad'i lokacin da ta hada ido da doctor sae duk jikin ta yayi sanyi domin ganin take yazo ne su tattauna kan plan d'in da suke shiri.
   Tafiya take zata haura sama doctor ya kalli Hakeem yace"kamar pinky bata jin dad'i fa"saurin kallon ta Hakeem yayi yace "me ka gani doctor? Baka ga jikin ta a sanyaye ba fuskar ta fayau kamar mara lafiya,wlh na tambaye ta doctor tace min wai bacci ne, a'a ba gaskiya bane akwai abinda ke damun ta.
   Hakeem na jin haka ya dakatar da ita ya jata suka zauna kan kujera sae kallon ta yake yace"pinky me yake damunki kike 6oye min? shiru ta mishi,Yace"please pinky say something.... may be ko ita bata san me yake damun ta ba,amma da alama zazza6i ke son kama ta bari naje cikin mota na d'auko allura ayi mata,ok doctor, nan doctor ya fita, Billy ta kalli Hakeem idanun ta cike da hawaye tace"Bobby bana son allura kuma ni lafiya ta qalau"no pinky da ganin ki ba kya jin dad'in jikin ki ki bari a miki allurà kinji,kuka ta fara mishi ya shiga lallashin ta.
  Doctor yazo ya same ta duk ta shagwa6ewa Hakeem tana kuka bata son allura.
   Yace doctor a ajiye zancen allurar nan bata so,, Hakeem... Please doctor wlh bana son jin kukanta ne da ace bana kusa da zan iya haqura domin in na tuna a gabana zaka soka mata allurar ina kallo to kuwa wlh ba mamaki zaka ji ina taya ta kukan,hmm shi dai doctor komai kasa cewa yayi sae kallon su yake cike da sha'awa yanda Hakeem ke lalla6a Billy kan ta daina kuka inda yake share mata hawaye cike da kulawa.
  Sae da tayi shiru yace"kin qarasa packing?girgiza mai kai tayi yace"to je ki qarasa kafin muyi break fast nida doctor sae muje asibiti mu duba Naini kafin mu tafi,
 nan ta tashi Hakeem ya bita da kallo cike da so har ta shige d'aki.
    ya maida duban shi gun doctor da ya saki baki yana kallon shi sae kace statue, Hakeem ya 6allah hannun shi tare da waving fuskar doctor,doctor yace "ai ina qasar banje koina ba kawai dai na zama speechless ne,kana abu kamar ba soja ba....kai doctor ajiye zancen soja koma nace ka ajiye zancen komai idan ana zancen so, na rantse maka doctor na bala'in kamuwa da son pinky abinda ban ta6a tunanin zai faru tsakani na da ita ba.....gaskyr ka Hakeem domin ba wanda zai sanku a da yayi tunanin zaku zamo haka,kuma kasan Allah,tun farko fa Naini bai mutu ba nine na tsara hakan sbd na samu na sasanta ta ku kafin ku koma Nigeria,domin nasan tabbas baza ka bari a kama pinky ba zaka d'ora laifin a kanka se nayi tunanin in taga hakan zata fara sonka... Au haba? Allah kuwa,oh no doctor ai tun farko ita ta fara sake min kafin ni amma naqi bata dama domin na d'auka wani  abu take shirin yi,,eyyah nifa duk a tunani na kai ka fara sake mata kuma tun lokacin da aka mata aiki na d'auka fishi take da kai bata daina ba,ashe kenan ko wata magana da naji tayi lokacin da police suka je da kai har na shiga mamakin ta, nasan ta fad'i haka ne sbd ganin kaqi sake mata bare ta sa ran zaku ci gaba da rayuwar aure... bari kawai doctor wlh yau cike nake da farin ciki zamu koma ga iyayen mu muna masu son juna duk da kuwa ba wanda ya furta ma wani so a cikin mu amma mun san muna son juna,
 har ma na qagu mu koma gida domin kawai na furta cewa ina son pinky a gaban iyayen mu sbd na sasu farin cikin da ban ta6a sasu ba a rayuwa,har surprise nake son bawa Billy na pink mota da nasa aka qera mata hadaddiya, kuma 6angaren mu gabadaya kwalliyar pink nasa akayi har da daki na kuwa,ba wanda yasan da hakan hatta su umma da Abba,
 Amjad kad'ai ya sani shida nasa aikin na kuma roqe shi kan kar ya fad'a ko su umma sun dawo sbd koda akayi aikin sunyi tafiya.
   Amma fa gaskiya Hakeem sae dae nace Allah ya d'ore soyayyar nan taku har jannatul Fiddausi,amin doctor na gode sosai fa domin kayi min addu'ar da tun da na fahimci ina son pinky nakeyin ta wacce nake matuqar fatar ta zama kar6a66iya sbd soyayya ta da pinky ina ji a jikina ta daban ce ba ko wace irin soyayya bace... But doctor muje muyi break fast kasan na qagu mu koma Nigeria domin dole a sake bikin auren mu ayi wanda muke cikin farin ciki ba kamar wancan ba... Au haba? Allah kuwa  kuma dole kaje domin na gayyace ka tun yanzu,,,inshaAllah kuwa zanje.
  Nan suka je kan dining suna break fast cike da nishad'i Hakeem sae fad'in yake yanda zai tsara bikin har yana fad'in kaf abokanan sa da sukayi karatu a turai sae sun zo.


Pinky kuwa tana d'aki sae wani  sabon kuka yazo mata domin ganin take suna can suna qara tsara plan d'insu na ganin Hakeem ya wulaqanta ta idan suka je Nigeria hakan yasa ta qudiri sae ta riga Hakeem aiwatar da plan d'in ta kafin shi.


Tafiya suke cikin mota sun fito asibiti zasu je airport sae kuka take ji sosai tana ta faman hana kanta domin duk jin take kamar su fasa tafiyar suyi zaman su har sae Hakeem ya fara son ta da gaske ko zasu koma.
   Hakeem ya fahimci yanayin ta sae duk yaji ba dad'i nan ya shiga bata labarai  masu ban dariya har ya samu ta fara sakewa har tana dariya.

 Fara'a take abinta har suka shiga jirgi.

 zaune take a 6angaren window jirgi na tashi ta kalli Hakeem cike da zolaya tayi pointing out of window tace"see Jennifer sae faman gudu take tana kiran ka,da wasa ya buge yatsar ya saka yatsar a bakin sa ya d'an ciza har sae da tayi er qara yace"idan kika sake nuna min Jennifer ko sae na mird'e yatsan, shi kuma bakin da ya sake furta Jennifer zan kama shi na tsotse tas tamkar alawa....a cikin jirgi mutane na kallon ka... to wa zai hana ni nida mata ta,bari ma kiga...dariya take ciki ciki tayi saurin 6oye fuskar ta a qirjin sa, a nan take se hawaye suka zubo mata sbd ko kad'an bata son ta tuna zata aiwatar da plan d'in ta har jin take kamar ta fasa taga shin me Hakeem zai yi amma gudun kar na Hakeem yasa ta baqin ciki da yawa zai sa ta fara nata kafin shi.
   Hakeem kuwa cike da farin ciki yakai  hannu ya qara rungumota tare da d'ora mata a kiss a ka yayinda ya furta a ransa
_"Allah ka nuna min mun isa gida lafiya domin na sanar da iyayen mu tsananin farin cikin da nake d'auke da shi a zuciya ta sannan na bawa Billyta surprise"_


To masu karatu muje muga shin wa zai riga wani  a cikin su.
    Nidai nace.....🙊oh no Nana saca only tace kar na fad'a😉 sae dae munga wa zai riga wani.
 Luv u😘.

*Billy giro😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 7:22 PM] ‪+234 810 038 8117‬: : [ 8/22/2016] Billy giro😊:
*👛BILLY PINKY DURLING👛*




*Na Billy giro😊*


*Page*
   *👛45&46👛*
A washe gari suka sauka guraren qarfe goma na safe kasancewar sun kwana a garin abuja.
    Suna fitowa Billy sae rarraba ido take ta inda zata hango su umma ai kuwa tana ganin su ta saki jakar hannun ta tafi da gudu ta fad'a jikin umma,Hakeem ne ya d'auki jakar ya biyo ta da ita inda ya same ta sae rungumar su Abba take wato mahaifin Hakeem da nata  sannan ta jewa qawar ta Feenah da ita ma tana gurin.
  Shima zuwa yayi cike da murna gurin iyayen shi suna tarbon shi,sae dad'i suke ji a ransu ganin Hakeem da Billy kowanen su yayi kyau ya qara haske kuma kallo d'aya zaka yi musu kasan suna son junan su sosai.


Nan suka tattara zuwa gida sae nan nan ake da su,sukayi zaune suna kwasar lafiyayen girkin da aka musu,gabad'aya kowa na kan dining sai santi suke zubawa sbd umman Hakeem mace ce wacce ta iya girki sosai.


Suna cikin cin abincin ne Abba sae kallon Hakeem yake wanda bakin sa yaqi rufuwa duk ya qagu su kammala cin abincin ya sanar da su albishir d'in da yake d'auke da shi.
   Abban Hakeem yace"wai Hakeem
wannan wane irin albishir ne da kake son sanar da mu, naga tun kuna Abuja ka kira ni ka sanar dani akwai albishir,kuma naga da alama ka qagu ka fada, eh wlh Abba amma dai nafi son mu kammala cin abincin tukun....gaban Billy ne ya bada ras _me Hakeem ke shirin sanar da su da yake farin ciki haka shine har da gaya musu kafin ya iso,koma mene ne ya kamata na riga shi,_

Nan ta ajiye farfesun kifin da take ci sbd ta daina jin dad'in abincin gabad'aya har wani  d'aci take ji a cikin bakin ta kamar wacce tayi zazza6i .
   Abban Hakeem yace mamanah ya akayi kar dai kice kin qoshi?eh na qoshi....oh wai ke har yanzu kina nan da rashin cin abinci"
 umma ce ta fad'i hakan.
  Billy dai bata ce komai ba sae qoqarin tashi take domin ta matsu ta bar gurin.
  nan ta wuce Hakeem sae kallon ta yake yana murmushi yayinda Feenah ke kallon shi sae duk taji soyayyar su ta fara bata sha'awa domin ta fahimci akwai so a tare da su.


Billy na shiga d'aki cikin sauri ta nemo takarda da biro hannun ta na rawa take rubutu yayinda hawaye ke ta faman zarya a fuskar ta d'agowar da zata yi taga mutum tsaye a kanta har sae da taji faduwar gaba
da sauri ta share hawayen da ke kan fukar ta tace"haba Feenah ya zaki shigo min daki ba sallama ni har kin tsorata ni wlh ... Hmmm lallai pinky me kike shirin yi ne haka naga kin wani rubutu saki kuma har uku...ba ruwan ki! ido ne kawai naki idan baza ki iya ba sae kisa kai, kuma wlh duk kika sanar da su Abba ni na rubuta shi kin san sauran... Meye sauran? Oho miki amma wlh se kinyi nadamar sanar da su da zakayi.
  Tana gama fad'a ta nad'e takardar zata fita Feenah ta jayo ta tace"pinky ya kamata ki tsaya kiyi tunani kafin ki aikata komai domin zakiyi babbar nadama idan kikayi hakan,meye matsalar ki da Hakeem bayan kallo d'aya za a yi muku a san kuna son juna.... Hm baki san komai ba Feenah don haka ki barni kawai nan tasa kai zata fice Feenah ta fizgo ta da qarfi tace"pinky kar kiyi haka fa!cikin tsawa tace"Feenah!wai so kike sae ya riga ni aiwatarwa kafin ni!da Allah sake ni na wuce!
 nan ta fizge hannun ta wanda yayi dai dai da shigowar umma tace"meye haka pinky me yake faruwa? Pinky tayi saurin 6oye takardar hannun ta tace"it's just about banci abinci ba take takura ni"to ya isa kizo Abbanku yana kira,
 nan umma taja ta aka bar Feenah tace"tabbas pinky idan kikayi kuskuren bada takardar nan sae na nuna miki kuskuren ki domin zan aure Hakeem kina ji kina gani dama abinda najima ina  nema ne.


Billy kuwa tafiya suke kan staircase gaban ta sae dukan uku2 yake zuciyar ta nata hana ta.
suna isa falo pinky ta sami guri ta zauña Abban Hakeem ya kalle ta yace"mamàna da alama kema akwai magana fal a bakin ki?eh Abba,,,to bari muji abinda yasa Hakeem ya tara mu a nan sannan kema ki fad'i taki ko,nan ta kalli Abba cike da damuwa,Hakeem ya lura da hakan yace"Abba ta fad'a muna jin ta,a'a kafa riga ta"Abban Billy ne yayi maganar,
 Hakeem yace"ba komai ta fad'a kawai Abba, yayi maganar ne yayinda yake kallon Billy cike da murmushi yace"talk pinky kinji muna sauraren ki,kalloñ sa take sosai tace a ranta
_"kamar alamu sun nuna da gaske Hakeem ke sona  har dai da na kalli qwayar idon shi but zan aiwatar da plan d'in naga bcs idan gaske ne yana sona to kuwa tabbas zai qaryata ni_
  Da qyar ta samu ta sai sai ta kanta ta fara magana cikin  natsuwa tace"Abba dama ba komai bane face abinda ya zama dole na sanar da ku, wanda nasan zakuyi baqin ciki da jin sa sae dai nace kuyi haquri domin nima ban so hakan ta faru ba,don ba yanda zan yi ne kawai.

Ba mu jima da zuwa new delhi ba, naso ace Hakeem ya bani dama mu kasance tamkar yadda kuke so ma'ana mu ajiye qiyayyar da muke yiwa junan mu, amma sae bai bani damar hakan ba ya nuna sam ba hakan a ransa kuma baya buqatar hakan, a nan ne yake sanar dani cewa na ma ajiye wannan zancen domin tun ranar da aka d'aura auren mu ya rubuta ya ajiye ni ba matar sa bace sam ba aure tsakani na da shi,da farko na d'auka  ya fad'a ne kawài se na basar da zancen inda nake ta qoqarin ganin mun dai daita tsakanin mu amma yana zille min.

To da haka ne wata rana ina gyara mishi d'aki ,
a cikin drawers din sa  ina tsara mishi wasu takardu  se na had'u da wannan takardar wacce ta nuna min tabbas ba aure tsakani na da Hakeem wato da gaske yake tun ranar da aka d'aura auren mu ya raba wannan auren domin har date ya saka........ Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Abba ne ya fad'i zancen yayinda ya zare hular kanshi yana kallon takardar wacce ke rubuce da saki d'ai d'ai har uku.
   Hakeem kuwa zumbur ya miqe cikin tsananin mamaki hannun sa na rawa ya kar6i takardar da ke hannun Abba yaga sak rubutun shi ne, kallon Billy ya shiga yi wacce ta tashi tsaye tana kallon shi sae fatar take ya qaryata zancen ta, shi kuma mamaki ya cika shi inda ya fahimci kenan dalilin da yasa pinky ta yaudare shi tasa ya koya mata rubutun shi,kenan soyayyar da take nuna mishi bada gaske bane,
_no!no!no pinky!_
   Yayi maganar ne a cikin ranshi yayinda yake kallon pinky idanun sa sunyi jajir duk jijiyoyin kansa sun tashi,kansa ne yayi mugun sara mishi yayinda rayuwar shi da pinky ta new delhi keyi mishi yawo cikin kai,
nan ya dafe kansa yana ja baya yana magana a ranshi cewa _"if yes i can't life any more with out u pinky!d only thing i will just go n kill my self!i will kill my self ryt now!_
  nan ya fita gidan kamar wani  mahaukaci su Abba suka bishi suna kiran shi, pinky kuwa kuka ke qoqarin zo mata ta tafi da sauri zata haura sama gabadaya idon ta ya rufe bata ganin komai tafiya kawai take kan staircase wanda har ta kai matakalar qarshe sae kawai jiri ya debe ta ta zube, nan ta shiga gangarowa  kan staircase.

Hakeem kuwa yana fita ya fad'a mota ya fige ta a haukace inda ya buge gate d'in gidan da qarfin tsiya  ya fita.

Umma wacce bata riga ta fita ba tayi saurin zuwa gun Billy tana taslima duk hankalin ta ya tashi domin koda ta gama gangarowa ta some goshin ta sae fitar da jini yake.
  Feenah ce ta fito da gudu jin yanda umma ke qwala mata kira.


Hakeem kuwa a bar zancen kawai domin yana fita ba ruwan sa da komai da ke kan hanya duk inda ya samu kad'a motar sa yake nan ya had'u da katuwar mota tayi cilli da motar shi wacce sae da tayi juyi uku kafin take tsayi.
  A rikice su Abba dake biye dashi cikin mota suka tsaida motar su suka fito.
   Tuni gurin ya cika da mutane akayi gaggawar fitar da Hakeem cikin mota ,nan aka tafi dashi *Hakeem Specialist hospital*
  wanda koda suka je Amjad yana kan Billy wacce su umma suka kai hakan yasa wani  likitan ya kar6i Hakeem.

Nan aka had'u su umma da Abba kowanen su cikin damuwa.

d'aki d'aya aka aje Billy da Hakeem d'aki ne na mutum biyu kacal sae dai kowanen su bacci yake.


Su Abba na zaune a d'akin ba mai cewa komai sae jiran farfad'owar su ake,kuma Alhmdlh ba wani  jin ciwo Hakeem yayi ba.
  Har akayi sallar zuhur ba wanda ya farfad'o a cikin su,nan su Abba suka tashi zasu je masallaci ita ma umma tace bari taje gida ta had'o musu abinci kafin su farfado,nan suka fita ya zamo Feenah kad'ai aka bari cikin d'akin.

Tana nan zaune ta fara ganin Hakeem na motsi cikin sauri taje ta kira doctor koda suka shigo Hakeem sae faman dannar kansa yake da ke mishi ciwo nan ya duba shi jiki sanyaye ya kalli Feenah wacce ya zaci er uwar hakeem ce yace"ki same ni office akwai wani  abu da zan gaya miki a game da Hakeem.

Ba musu ta bishi ta samu guri ta zauna, nan ya cire gilashin da ke idon sa tare da furzadda iskan bakin shi yace"am sorry to say sae dai kuyi haquri da tsarin ubangiji domin a binciken da nayi kafin Hakeem ya farfado na same shi da matsala guda biyu da ya samu a sanadiyar buguwa, amma ban fad'a ba sbd ina so na qara tantancewa idan ya farfado,koda ya farfado naga haka d'in ne a bisa wasu tambayoyi da na masa.
  Matsalar farko ita ce Hakeem ya manta komai wanda ya faru wata biyu da suka wuce ma'ana duk abinda ya faru a wata biyu da suka wuce bazai tuna su ba.
   Cike da damuwa Feenah ke kallon shi inda ta shiga wani  lissafi cikin qwaqwalwar ta, tace doctor don Allah ina so kar ka sanar da kowa wannan matsalar,sbd zaka d'aga hankalin iyayen mu don Allah doctor,,,gsky wannan matsala ba abin 6oye wa bace dole a sanar da iyayenku ko yanzu don ina sauri zan fita  yasa nace kizo na sanar da ke amma mahaifin ku ne ya dace nayi wa wannan bayanin ba ke ba..but doctor na fi so na musu bayanin da kaina Allah bana so hankalin su ya tashi, tayi maganar ne cikin marairaiwa,yace to shike nan nayi miki alqawari bazan sanar da kowa ba, nan ta mishi godiya ta fita cike da jin dad'i a ranta  kan ta sami wata damar da ta barwa kanta sani.

Da sauri doctor ke qoqarin kiran ta sbd bai gaya mata matsala d'aya ba sae dai kuma ya basar domin d'ayar matsalar ta wuce ya sanar da feenah ita sae dai mahaifin su.

koda ta koma dakin ta samu Billy ta farka sae kallon Hakeem take da ya juya bayan shi wanda takaici ya cika shi yana tunanin me ya faru da shi da har yazo asibiti aka kuma had'a shi da pinky d'aki d'aya.
   

Shigar Feenah keda wuya sae ga su umma sun dawo har da su Abba.
    Nan Hakeem ya juyo domin ya tambayi abinda yasa aka  kawo shi asibiti sae dae ganin fuskar Abba a d'aure yasa yayi shiru.
     Gurin Billy Abba ya nufa yana mata sannu kafin yake maida duban shi gun Hakeem  wanda yace"Abba wai me yake faruwa ne...kar ka raina mana hankali ai kafi kowa sanin abinda ya faru.
  Nan Abba ya fitar da takardar saki yace gaya min gaskiya kai ka rubuta takardar ko kuwa?Abba ban fahimce ka ba ita wannan takardar a ina ta fito....a gidan ku ta fito d'an rainin hankali!ka gaya min wa yayi wannan rubutun nace!?
  Nan Hakeem ya kar6i takardar yana kallo yaga tabbas rubutun sa ne kan cewa ya saki Billy wani irin dad'i yaji har cikin ransa,amma kuma bazai iya tuna lokacin da yayi shi ba shidai kawai abinda ya sani yasan an d'aura aure tun daga haka ba zai iya tuna wani  abu ba.

    Nan ya d'ago yana kallon Abba yayinda Billy ta tsare shi da kallo domin taji me zai ce.
  Yace"Abba wannan ai rubutu na ne kuma ni nayi shi.
 
*Billy giro😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 7:34 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [ 8/23/2016] Billy giro😊:
 *👛BILLY PINKY DURLING👛*




*Na Billy giro😊*



*Page*
   *👛47&48👛*
Hawaye ne suka zubo zar a kumatun Billy yayinda Abba ya kar6e takardar a hannun Hakeem yace"tabbas Hakeem yau ka nuna mana ba mu isa da kai ba duk da kuwa cewa mune mahaifan ka,amma ina mai tabbatar ma daga yau ba mu ba kai mun yafe ka kaje can ka nemi wasu iyayen!....a'a maganar hakan bata taso ba haquri zakayi aure dai ya riga ya rabu sae muyi haquri da hukuncin ubangiji, Abban Billy ne yayi maganar, Abban Hakeem yace"Sam ba zai yiyu ba,dole yabi hukuncin da na yake idan kuma yaqi to  ina mai gaya ma muddin ya sake sa qafar sa a cikin gidana ba abinda zai hana na tsine mai kuma ko kai ban yarda yaje gidan ka ba!kai gabadaya kaf dangin mu ba inda na yarda yaje!.
   Haba yaya.....bafa zanyi magana biyu ba! domin ban yanke hukunci ba sae da naji da bakin sa shi yayi sakin,
 duk da kuwa nafi kowa sanin rubutun sa amma ganin tashin hankalin da ya shiga a lokacin da mamanah ta bada takardar na d'auka cewa akasi aka samu sae gashi kunji abinda ya furta da kunnen ku ba wani akasi...amma yaya ya kamata ka fahimci cewa yayi nadamar hakan shiyasa ya shiga tashin hankali har yana qoqarin hallaka kanshi....ai baiyi nadama ba yanzu yake shirin yinta domin ya rasa mamanah har abada koda kuwa tayi wani  auren ta fito.

Gabada'ya Hakeem jin zancen yake wani  iri ga kuma tashin hankalin da ya tsinci kan shi kan hukuncin da Abba ya yanke mishi,nan yaji gara ya fad'i gaskiya bai san lokacin da yayi rubutun ba ko Abba zai sassauto da hukuncin da yayi mishi.
  Yace"Abba don Allah kayi haquri wlh bansan..... Wlh kar ka kuskura kace zaka sake furta wata kalma a nan!...amma Abban Hakeem ya kamata kayi haquri ka sassauta hukunci nan yayi tsauri da yawa,umman Hakeem ce tayi maganar cike da lallashi.....yace bafa zan canza komai ba idan so kike ki kasance tare da shi kya iya ki bishi,daga haka tayi shiru ganin abin yana so yafi qarfin ta.

 Billy kuwa ba abinda take face kuka ganin take kenan dai da gaske ne Hakeem ba son ta yake ba yayi haka ne kawai don plan d'in ta ya koma kanta gashi yanxu ya barta da tsananin son da take mishi sae duk taji da ace tun farko bata tsara plan d'in ba da duk hakan bata faru ba.

Feenah kuwa shiru tayi tana bin kowannen su da ido yayinda take saqe saqe a cikin ranta.

Abba ne ya buqaci a d'auke Billy daga dakin kuma bai yarda kowa ya zauna gurin Hakeem ba,
 nan suka tattara suka koma d'akin da aka canzawa pinky ba don sun so hakan ba, musamman pinky wacce taji tamkar an raba ta da wani  sashe na jikin ta,kuka kawai take umma na rarrashin ta.

Da dare guraren 11:30 Feenah ce ta shigo asibiti ba tare da kowa ya sani ba ta nufi d'akin Hakeem ta samu ba kowa a ciki hankali tashe taje neman shi cikin asibiti.

A 6angaren Billy kuwa kwance  take kamar mai bacci amma hankalin ta na kan umma dake ta nafilfili inda ta qagu umma ta kammala ko zata yi bacci ita ta samu taje dakin Hakeem.
   Sai 12 ta samu umma ta kishingid'a nan ta lalla6a ta tashi tana d'ingishi kasancewar qafar ta da ke ciwo,
 bata zarce koina ba sae d'akin Hakeem ita ma bata sami kowa ba nan ta duba toilet baya nan ta fito hankali tashe sae ta hango er guntuwar takarda kan drawer hannun ta na rawa ta d'auki takardar tana gama karantawa ta fashe da kuka sae ga umma ta shigo nan ta fad'a jikin umma,nan umma ta hango takarda a hannun ta,ta kar6i takardar tana karantawa, haquri ne Hakeem ya bawa mahaifin sa sosai sannan yace"Abba na tafi kamar yadda ka buqata amma a ko yaushe ina mai sauraren afuwar ka Abba domin na samu na dawo gare ku.
  Da sauri umma ta share hawayen da suka zubo mata,nan takardar ta fad'i tabi iska cikin sauri umma ke bin ta sbd tana son Abban Hakeem ya ganta ko hakan zai sa ya haqura.

Feenah ce kan hanyar dawowa d'akin Hakeem ta had'u da paper inda ta hango umma cikin sauri tana bin takardar,
da sauri Feenah ta rufe fuskar ta da mayafi kar umma ta gane ta,ta kuma yi saurin d'auke takardar ta bar gurin.

Sae da ta sami gurin la6ewa sannan ta tsaya ta karanta.
 damuwa ce fal ta bayyana a fuskar ta yayinda ta yayyaga takardar ta watsar taje taja motar ta tabar asibiti.

Umma kuwa cike da rashin jin dad'i ta juya ganin bata ga takardar ba.

Taje taja Billy tana rarrashin ta suka koma d'aki.


Washe gari tun da safe aka sallami Billy sbd yanda ta matsa a sallame ta.


Suna zuwa umma bata zarce koina ba sae d'akin Abba,
 ta sanar dashi cewa Hakeem fa ya tafi da gaske, yace"to meyasa baki bishi ba a lokacin da zai tafi domin na fahimci so kike ki bi shi.
   Abban Hakeem don Allah kayi haquri baka ga yanda yaron nan ya baka haquri sosai a cikin takardar da ya ajiye kafin ya tafi kuma ya nuna cewa a ko yaushe yana jiran saqon afuwar ka domin ya samu ya dawo gida....ina takardar take? ta 6ata a asibiti amma sosai naso ace kaga takardar domin  ka karanta da kanka,amma tun da na gaya ma don Allah kayi haquri, nan "yace naji zan yi tunani akai"
amma ya fad'i haka ne kawai don ya huta da ita, sbd ganin yake ba wata takardar da Hakeem ya ajiye tausayi ne kawai irin na uwa yasa ta tsara hakan.


Haka umma tayi ta sa ran dawowar Hakeem amma shiru har yau sati d'aya.


Pinky ce zaune a falo wacce duk tabi ta rame ta ya kuce kallo d'aya zaka yi mata kaji baka son qara na biyu.

Tunda suka dawo ta maida falo gurin zamanta ba don komai ba sae don sa ran dawowar Hakeem a ko yaushe,
 ta zama tamkar wata securityn bakin qofa da taji knocking ko door bell har tuntu6e take garin sauri taje ta bud'e ko za taga Hakeem ne ya dawo.


Ko yanxu zaune take  sae kallon qofa take duk ta zama abin tausayi wacce duk ta tuna ita ce silar faruwar komai sae tayi ta zubar da hawaye cike da nadama,ko yanzu kuwa hawaye ne a fuskar ta se taji door bell nan tayi saurin share hawayen  ta tafi da sauri.

Tana isa bakin qofa ta rufe idon ta domin bata son ganin ba Hakeem bane,kamar yadda take faman gani kullum.
  Bud'e qofar take yayinda take ta addu'a a ranta Allah yasa idanuwanta su ganar mata abinda take son gani.

Sae da ta bud'e qofar sannan ta shiga bud'e idon ta a hankali, amma bata yarda ta fara da fuskar ko wane ne ba, da qafafun shi ta fara sannu sannu take tafiya da idon ta sama inda ta ga hannun shi riqe da trolley bag, ta tafi har zuwa fuskar shi, ba yabo ba fallasa take kallon shi haka shima wanda ke tsaye yake kallon ta kafin yake cewa"pinky"tace "Naini"

*Billy giro😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 7:40 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [ 8/24/2016]


*👛BILLY PINKY DURLING👛*






*Na Billy giro😊*



*page*
    *👛49&50👛*
Cike da rashin jin dad'in ganin ba Hakeem bane ta mishi sannu da zuwa kafin take bashi hanya ya shigo.


Sama ta haura taje ta sanar da umma da Abba suka fito.
  Naini ya zame kan kujera tare da russunawa ya gaishe su.
  Bayan sun amsa Abba ke cewa yanxu nan muka gama waya da mahaifin ka yake tambaya ta ko ka iso nace tukuna, ashe har ka iso kana ma cikin gidan,
 eh Abba,,,
  To ya hanya? Alhmadlh,,
  Ya karatu koda yake yanzu ka kammala? Eh shekaranjiya jiya muka kammala inshaAllah,, to ubangiji Allah ya bada Sa'a akan komai,,,
amin Abba.

Umma dake sauraren su ta qwalawa Billy kira sae gashi ta fito, tace"baki ga Naini yazo ba amma shine kika shige d'aki, je ki kawo masa abin motsa baki,
 ba musu ta nufi hanyar kitchen Naini sae kallon ta yake, umma da Abba duk sun lura da hakan, umma tace"Naini kaga yanda Billy ta zama abin tausayi duk tabi tasa abun a ranta sosai,duqar da kanshi yayi qasa cike da damuwa duk da baisan abinda ya faru ba.


Nan su Abba suka fice Billy ta kawo ma Naini abinci Bayan ya gama yace"pls ki sanar da Abba ina so zanje granny house, kuma gashi bai kar6i saqon da Abba yace na bashi ba.
  Nan taje ta kira Abba daga nan ta wuce d'akin ta.


Washe gari da safe guraren 11:30,Naini ne ya shigo gidan ya sami Billy da Amjad a falo, umma ta riqe Billy ana mata allura sae kuka take.
  Har cikin ranshi yaji abun amma yayi saurin hana kanshi sbd so yake ya cire Billy a ransa.

Sae da ya gaida su sannan umma taja Billy suka shiga daga ciki, Naini ya kalli amjad da ya sharewa en guntayen hawayen shi, Yace"Amjad lafiya"
  Nan amjad yaja hannun Naini suka fito harabar gidan yayinda suka jingina a jikin motar Naini.
   Cike da damuwa ya kalli Naini yace"na dad'e ina neman abokin da zai taya ni baqin ciki sae gashi Allah ya kawo ka, kai da nasan kayi zama na kusan wata d'aya a new Delhi tare da su pinky, zan fi jin dad'in wannan zancen da kai bcs har ko yaushe abin yana d'aure min kai sosai,shin ko kai kayi mamaki kan abinda ya faru tsakanin pinky da Hakeem? na me kenan? kar kace min baka san me yake faruwa ba,ni ban san wani  abu da ya faru ba ina dai son na sani,,,,da kamar mamaki kuwa domin a yanda Abban Hakeem yaji baqin cikin faruwar abin na tabbatar ya sanar da mahaifin ka,,,ba mamaki ya sanar da Abbana amma banji a bakin shi ba kuma banyi mamakin hakan ba sbd Abba bai cika son gaya min abinda zai sani a damuwa ba bare a lokacin ina exams dole zai kiyaye abinda zai sa na kasa maida hankali na kan karatu,kuma muna gama exam yace zai aiko ni Nigeria banso hakan  ba sbd wani  abu da nake son hanawa zuciya ta,amma ba yanda na iya dole nazo.

Ajiyar zuciya Amjad ya sauke ya shiga sanar da Naini kaf abinda ya faru bayan dawowar su pinky.

Zaro ido Naini yayi yana kallon Amjad sae duk ya shiga damuwa sosai idanun sa suka cika tap da qwallah domin sonda Naini yake yiwa Billy so ne wanda baya son Billy ta rasa wani  abun da take so, koda kuwa shi a gurin shi baqinci ne, yafi buqatar hakan.

  Yace"Amjad saki fa kace kuma d'ai d'ai har uku Hakeem yayi wa pinky?sosai kuwa....no this can never happen bcs Hakeem yana son pinky sosai ni shaida ne... Hm ba don kafi ni kusanci da su ba,da sae dai nace nafi kowa sanin hakan,amma sae gashi naji labari a bakin wacce abin ya faru a gaban ta wato Feenah qawar pinky,amma duk da hakan naso ace naji ainihin yanda abin ya kasance a gun su umma amma kuma se naga meye amfani tunda aure ya riga ya rabu ba wani  gyaran da za a yi a kai,kuma qarin takaici ne kawai idan na tuntu6e su da zancen,sbd kan takaici Abba fa ya kori Hakeem tun ranar da abin ya faru gashi yau sati d'aya bashi ba labarin shi,duk inda nake sa ran zan ga Hakeem na neme shi na rasa.
  Naini yace"ya salam! wannan wane irin abu ne haka,nagode Amjad da ka sanar da ni wannan abun zan shiga daga ciki.

Koda ya shiga falon ba kowa yayi tsaye ya rasa me zaiyi duk tausayin pinky ya cika shi.
 Fitowa yayi yaja motar shi ya bar gidan

2 days Naini na shigowa gidan baya samun pinky haka ko yau umma kawai ya samu a falo, sae da ya gaisa da ita yace"umma halan ina pinky take ne? Him!Billy tana 6angaren Hakeem nan ta mayar gurin zuwan ta ko yaushe hatta bacci da ace Abban Hakeem zai yarda da can zata riqa bacci,domin har fad'a yayi mata kan ta daina zuwa can,amma yana fita zata saci jiki taje.
    Shiru naini yayi can yace"umma ashe  wani abu marar dad'in ji ya faru tsakanin Hakeem da pinky shiyasa na sami pinky duk tabi ta rame,cike da damuwa umma tace"wai dama baka ji ba?eh umma sae daga baya nake ji a bakin Amjad,amma umma don Allah da kun haqura kun bar Hakeem ya dawo gida,,,,,
Naini ai Abban Hakeem ne yaqi haqura har yanzu,nayi ta bashi haquri,
 yace wai na bar shi zai yi tunani akai, wanda duk a tunani na,zai ce Hakeem ya dawo amma naji shiru har gashi yanzu sati d'aya,amma inshaAllah yau zan tuntu6e shi da zancen dama nayi shiru ne kar yace na cika takura shi.
   To umma ina ce an san inda yake  koda Abba ya haqura, shine matsalar gsky bai fad'i inda yaje ba kawai yace yana jiran saqon afuwar Abban shi domin ya samu ya dawo, daga haka bai yi wani  baya ni ba wanda koda Abban shi ya haqura za'a je a sanar da shi.
   To umma inshaAllah ni zan shiga neman shi koma ina ne, domin a samu damuwar da pinky take d'auke da ita ko zata ragu,, him!Naini damuwar Billy damuwa ce da take bani mamaki ta riga tasan da sakin nan tun kafin suxo,amma sae zuwan su ne ta shiga damuwa sosai koda yake dole ta shiga damuwa sbd korar Hakeem da Abban shi yayi.
  Haka ne zanje na ganta, yana gama fad'a ya fita bai zarce koina ba sae 6angaren Hakeem,da sallamar shi ya bude d'akin, Billy dake kwance  ta tashi domin ganin wane ne, ajiye photon Hakeem dake riqe a hannun ta tayi.

Ta zauna da kyau tana mai kallon Naini,yace"pinky naji abinda ya faru na kuma yi baqin ciki sosai, na kuma yi mamakin yanda Hakeem ya aiwatar da hakan, amma ina mai jajanta miki kan kiyi haquri ki barwa Allah komai, kuma duk da nasan aure ya riga ya rabu tsakanin ki da Hakeem ya zama dole na nemo miki shi duk inda yake domin ko kad'an bana son ganin ki cikin damuwa, hakan nasa ni damuwa sosai.
  Sosai taji dad'in kalaman Naini ta share hawayen da suka zubo mata tana ji kamar ta sanar da Naini ita ce ta rubuta sakin ba Hakeem ba, amma kuma tana fargaba sbd wani  dalili da ta barwa kanta sani.
  Godiya kawai tayi mishi, ta tashi suka fito daga d'akin suna cikin tafiya suka hadu  da Abba a harabar gidan, nan Abba ya kira su, pinky taje cike da jin nauyin Abba sbd tasan ya hana ta zuwa d'akin Hakeem,nan ta duqar da kanta qasa bata yarda ta had'a ido dashi ba, yace"mamanah a ko yaushe lalla6ar ki nake kan ki cire damuwa a ranki kan wanda sam bai dace ace kin damu a kanshi ba.
   Amma kije inshaAllah wannan damuwar ta kusa yaye miki domin na kusa kawo qarshen ta inshaAllah, wani  irin dad'i Billy taji a ranta domin ganin take Abba zai ce da Hakeem ya dawo.

 Hakan yasa ta d'an fara jin sauqi a ranta duk da tasan cewa ko ya dawo ba zai kula ta ba,amma tafi buqatar hakan da ace baya gidan.

Kwana biyu taci gaba da sakewa har tana fitowa shan iska yayinda Naini ke zama yana taya ta fira amma duk yanda yaso pinky tayi dariya baya samun hakan sae dai tayi ta sauraren shi ba eem ba um um.
  Ko yanzu zaune suke sae labari yake bata tana sauraren shi,a cikin labarin ne ya d'auko zancen Hakeem hakan yasa ta qara maida hankalin ta tana kallon shi,nan ya bata labari kan wata rigimà da suka ta6a yi  shi da team d'in sa da na Hakeem a new delhi kan ball.
   d'an guntun murmushi ne ya bayyana a fuskar ta domin a cikin rigimàr su akwai dariya sosai har dai team d'in su Hakeem,sae duk taji tana son yin ball amma tana tuna Hakeem ya hana ta wasa da Naini nan tayi saurin cire ball d'in a ranta.
   Abba ne ya biyo yana kallon su cike da jin dad'in ganin Billy ta fara sakewa nan suka gaida shi kafin yake shiga daga ciki.

Abba bai jima da shiga ba sae ga Feenah ta kunno da motar  ta,bayan Feenah ta gaisa da Naini ne suka shiga daga ciki shi kuma ya ja  motar shi ya bar gidan.

Suna shiga d'aki pinky ta duba fridge d'in ba lemu nan ta fito da niyar taje downstairs ta d'auko fad'an da taji Abba yana yi ne ya dakatar da ita inda umma ke masa magana kan Hakeem yace"ai ba qaramin yaro bane don haka sae na gama abinda ke gabana tukun, domin yanzu bani da burin da ya wuce naga mamanah ta gama idda na auradda ita,domin ta huce takaicin Hakeem,,,, Haba Abban Hakeem yanzu har sae Billy ta gama idda sannan za'ayi zancen Hakeem....to me ya rage ta gama idda in banda sati biyu da en kwanaki,tunda tun ranar da aka d'aura auren su ne ya sake ta, kuma a binciken da nasa kimin kince mamana ta sanar dake ba wani  abu da ya ta6a shiga tsakanin ta da Hakeem har suka dawo,,,but Abban Hakeem dawa kake shirin had'a ta aure baka gudun abinda ya faru ya sake faruwa?
Ba abinda zai faru sai alheri inshaAllah domin wanda zan had'a ta aure dashi  yana matuqar sonta kuma ita ma alamu sun nuna zata so shi,kuma nasan mamanah baza ta bani kunya ba ko don abin da Hakeem ya mata,,, amma Abban Hakeem wane ne kake shirin had'a ta aure da shi? Naini wanda ko yanzu na same shi da mamanah suna fira a waje sae murmushi take abinda na jima ban gani ba tun faruwar wannan abun,don haka da mamanah ta gama idda zan kira ta na sanar da ita abinda muka yanke shawara nida mahaifin ta da kuma mahaifin Naini......tamkar saukar aradu Billy take jin zancen da gudu ta koma d'aki ta fad'a jikin Feenah tana kuka.

 Tace"na shiga uku Feenah na aikata abin da nazo ina babbar nadama akan shi,gashi sae da kika hana ni amma naqi,,,, mene ne pinky? Aure Abba ke qoqarin had'a ni da Naini kuma kinsan akwai auren Bobby a kaina, kuma ina jin tsoron sanar dasu hakan domin na tabbatar idan Abba na yaji hawan jinin sa zai iya tashi,kuma kinsan ciwon Abba in ya motsa tamkar ba zai rayu ba ina gudun na fad'a naje na rasa Abba na a wannan karon.
  Ajiyar zuciya Feenah ta sauke ta shiga sharewa pinky hawaye tace "zan baki wata shawara pinky amma bana son kowa yaji.
   Nan ta rufe ko wacce window ta d'akin ta kuma sakawa d'akin key yayinda ni Billy giro na rasa inda zan laqa kunne na naji shawarar da Feenah zata bawa pinky.
  Haka suka qaraci shawarar su banji komai ba.

Tun a lokacin Billy ta shiga tunanin shawarar da Feenah ta bata gashi yanzu har ta gama idda a yanda su Abba ke tunani.


Zaune take a gaban su Abba wato Abban Hakeem da Abban ta, Abban Hakeem ne yace" mamanah mun kira ki ne domin wata shawara da muka yanke, shawar ita ce tun da kin gama idda muna so zamu had'a auren ku da Naini sbd zaman da kike yi ko yaushe cikin damuwa yana damun mu sosai amma ba dole a cikin wannan auren sae da amincewar ki duk da cewa ba mu yanke shawarar ba sae da muka tabbatar cewa Naini yana matuqar sonki inda muke sa ran zaman ki da shi zai yi kyau sosai,amma don Allah mamanah idan kin san ba kya ra'ayin auren nan kar ki takura kanki.
   Duqar da kanta tayi cike da tunanin shawar da Feenah ta bata,hawaye ne suka zubo mata tayi saurin share hawayen ba tare da su Abba sun lura ba tace"Abba ni yanzu bani da wani  za6i duk abinda kuka yanke akaina dai dai ne, ma'ana ina nufin na amince zan auri Naini.


Hm!ni Billy giro kan takaici na kasa tsayi na ida kwaso muku rahoton inda naji kamar ma na daina kwaso muku rahoton gabad'aya! domin cike nake da mamaki da kuma takaicin wannan wace irin gurguwar shawara ce Feenah ta bawa pinky da har ta yarda zata yi aure kan aure.
   Mtsw muje zuwa dai muga ko shawarar Feenah zata haifar mana d'a mai ido.


*Billy giro😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 7:48 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [8/25/2016] Billy giro😊:

*👛BILLY PINKY DURLING👛*





*Na Billy giro😊*



Assalamu Alaikum my lovely fans😊
   I'm still in love with u duk da naga irin maganganun da wasun ku suka min da basu dace ba a game da page d'in jiya, sun fad'a a grps har ma ana bi na a private, daga mai cewa marubuciyar ta bata haushi sae masu cewa sun daina karatun novel d'in da dai sauran su,
 amma ko kad'an ban bawa zuciya ta damar fushi da ku ba sbd nasan son Hakeem da Billy ne yasa ku aiwatar da hakan kuma ko ba haka ba ku masoyana ne kuma nima ina sonku sosai, amma ya kamata ku tuna ni musulmace bazan aiwatar da abin da kuke tunani ba,kuma ina son don Allah ku riqa haquri kuna bin komai sannu a hankali har ku cimma ribar shi,
 domin komai na duniyar nan sae da haquri.

Cikin muryar rarrashi nake cewa "I'm really really sorry my fans bcs a gaskiya bazan canza tsarin novel d'ina ba,
 zan ci gaba da tafiyar da shi kamar yadda na tsara tun farko sae dae nace wad'an da zasu iya ci gaba da bina kuci gaba da biyoni domin jin ci gaban labarin har muga munkai ga qarshen sa muna masu rai da lafiya inshaAllah.
     Luv all my fans muah💋😘



*page*
   *👛51&52👛*
Alhamdulillah Allah yayi miki albarka mamanah kina iya tashi ki fice.
   Jiki sanyaye ta tashi cike da tunani kala kala a ranta.
   Tana zuwa d'aki ta fad'a kan bed tare da fashewa da wani  irin kuka mai tsima zuciya.

Bayan kwana biyu da faruwar hakan kwance  take kamar mara lafiya domin tunda tace ta amince da auren Naini duk ta cika da tunani har bata iya aiwatar da komai na kirki.

Umma ce ta shigo d'akin da sallama Billy ta amsa yayinda take qoqarin tashi zaune.
  Umma tace"Abban ku yace a sanar da ke cikin satin nan za'a yi d'aurin aure inshaAllah.....zumbur Billy ta miqe tace"na shiga uku!.....meye na shiga uku?umma ina da auren Bo......am ina nufin auren yayi kusa umma ban zaci cewa da wuri haka bane.
  Murmushi tayi tace"haba Billy sae kace wani  tashin hankali ki kwantar da hankalin ki wannan auren ba auren da zakiyi baqin ciki kamar wancan bane inshaAllah.
  Komai Billy ta kasa ce ma umma.
  Umma na fita tayi saurin jawo wayar ta ta kira Feenah tana sanar da ita cewa "feenah ashe cikin satin nan fa za'a d'aura aure kina ganin kuwa komai zai yi dai dai?
Feenah ta shiga kwantar mata da hankali tace inshaAllah komai zai yi a yanda muke so kar ki damu kedai kawai kiyi shiru da bakin ki kar ki yarda ki furta akwai auren Bobby akan ki, sbd kinsan fad'ar hakan ba mu riga mun kammala komai ba matsalar zata yi yawa.

   Duk da jin haka dai hankalin Billy sam yaqi kwanciya ji take kamar taje ta fasa qwan kowa ya huta amma kuma da ta tuna maganar feenah gaskiya ce sae ta sami kanta da fasawa.

Hm abun kamar wasa ni Billy giro sae ganin ikon Allah nake domin bakin rai Billy tayi shiru sae shirye shiryen aure ake sae dae kwata kwata hankalin ta yaqi kwanciya ko yaushe cikin kiran Feenah take,Feenah kuwa sae haquri take bata tana kwantar mata da hankali.

Yauce ranar d'aurin aure gida ya cika maqil ai kuwa duk inda hankalin Billy yake ya tashi domin kallo d'aya zakayi mata kasan hankalin ta ya tashi gashi tana kiran wayar Feenah amma bata samu.
 
Umma ce ta shigo d'akin ta sami Billy duk tabi ta ya mutse d'akin kamar d'akin mahaukata umma tace"meye haka?
 Komai kasa cewa tayi domin ita kanta bata san dalilin yin hakan ba,kawai ta tsinci kanta da yin hakan.
  Umma tace"dama nazo na sanar da ke ne an fasa d'aura aure a yau ana sa ran sae gobe da safe za'a d'aura amma  idan iyayen Naini sun sami isowa yau to za'a d'aura auren a yau.
 
Nan hankalin pinky ya d'an kwanta sae kallon umma take dake shirya mata kaya ko qaqa taso yin waya da Feenah domin taji ya ake ciki.

Umma na gama shirya mata kayan ta fita  nan Billy ta shiga kiran Feenah amma har dare bata sami Feenah ba.

Har tayi shirin bacci amma ta kasa kwanciya sae faman ci gaba da kiran Feenah take amma still wayar har yanzu bata shiga,cike da takaici ta fashe da wani irin kuka  had'i da jefar da wayar sannan ta fad'a ruf da ciki kan bed tana kuka,
 umma ce ta shigo d'akin cikin sauri tace"tashi tashi sauri ake za'a shirya ki!a rikice Billy ta tashi tana kallon umma da ke riqe da kayan amare, bata saurari me Billy zata ce ba kawai ta shiga shirya ta.

Tsaf ta shirya ta kyace amaryar India duk tabi ta feshe mata jiki da turare sae qamshi ke tashi a jikin ta gashi tayi bala'in kyau.

Ba wata wata taja hannun ta suka fito falo inda taga falon cike yake maqil da abokanan ta na school,sae binsu da ido take koza ta ga feenah bata ganta ba sae jin tayi sunja hannun ta suka fita da ita harabar gidan motoci ta gani jere yayinda aka wangale qatoton gate d'in gidan domin basu hanyar wucewa.

 Hankalinta bai gama tashi ba sae da aka saka ta mota taga Naini sae murmushi yake bakin sa baya ko rufuwa, duk ta rikice tana tunnin ko an d'aura aure ne bata sani ba shine ake shirin kai ta.
   At all ta nemi kuka ta rasa sae kawai taji an tashi motoci saurin kallon Naini tayi sae taji kamar wacce aka rufewa baki ta kasa ce mishi komai.

Tafiya ake yayinda hankalin ta ke qara tashi sae dube dube take kan titi kamar wacce ke neman wani  abu,
 kamar a mafarki ta hango motar Feenah bata san lokacin da tace da driver "stop d car!
 bata wani  bari motar ta qarasa tsayi ba ta fito kamar wata zautacciya yayinda ta hango motar Feenah ta tsaya wani  ya fito cikin motar sae mashalo yake kamar d'an giya ya tafi suuu zai fad'i,da sauri ta kwashe bazajjen idian skirt d'inta wanda le6ar bayan shi naja har ga qasa ta fara gudu cike da son ta isa gurin motar Feenah kafin wannan gayen ya fad'i.

gabad'aya mutane suka firfito cikin mota suna kallon ikon Allah.

Billy kuwa sae gudu take amma kafin ta isa har gayen ya fad'i kansa ya bugi qasa da sauri ta durqusa kan guiwoyin ta ta tallaboshi jikin ta tana jijjga shi tana kiran sunan shi,
 da qyar gayen da ke dafe da kanshi ya bude ido yana kallon ta,haka da qyar ya samu ya furta cewa"u know i'm really luv u pinky but why u do dis to me?
kuka ne yazo mata mai had'e da dariya tana kallon shi da mamaki tace"my real Bobby"ta fadi hakane yayinda ta rungume shi sosai a qirjin ta, ta d'ago shi tana kai mishi kiss sauri sauri ta koina cike da tsananin farin ciki, nan ta qara rungume shi ta fashe da kukan farin ciki tace"tank u God! tank u Feenah,tank u so much.
   Nan Feenah ta qaraso gurin su tana share hawaye cike da murmushi mai had'e da dariya se kallon Hakeem da Billy take cike da ban sha'awa,haka naga shima Naini yazo yayinda murmushi ke dauke a fuskar shi yayi tsaye a kansu wanda kallo d'aya nayi mishi na fahimci shima sun bashi sha'awa sosai.


*Billy giro😊[truncated by WhatsApp]
[9/22, 7:49 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [, 8/26/2016] Billy giro😊:

 *👛BILLY PINKY DURLING👛*




*Na Billy giro😊*


*page*
    *👛53&54👛*
D'ago kanta tayi tana mai qara godewa Feenah.
   Feenah tace"bani kad'ai zakiyi wa godiya ba,ta nuna Naini tace"kin ganshi a tare mukayi komai"
  Da mamaki pinky ta kalli Feenah kafin take kallon Naini wanda yayi murmushi tare da duqar da kanshi qasa sbd hawayen da yaji suna qoqarin zo mishi
Feenah tace"tabbas dashi mukayi komai kar kiyi mamaki domin shi masoyin ki ne na gaske wanda baya son ganin kin shiga qunci.
  A ranar bayan na gama yi miki bayani a d'aki na fito cike da tunanin yanda zan fara aikin ni kad'ai haka nake ta faman magana zan shiga mota sae kawai naji magana kamar daga sama yace"ba wanda ya dace kiyi aikin nan dashi face ni, nayi masa kallon mamaki, yace"kar kiyi mamaki akan komai indai game da soyayyar da nake yiwa pinky ce zan iya yin komai na ganin farin cikin ta ya dawo koda ni a gurina ba farin ciki bane, bare tun a new delhi na haqura da komai domin na fahimci ba wanda ya dace da pinky face Hakeem shiyasa naji baqin cikin rabuwar su, amma yanzu bani da wani  baqinci sae na rashin sanin inda Hakeem yake domin naji duk maganar da kuke ta waya,
 bcs  na kira pinky ta ta d'aga wayar a cikin rashin sani shiyasa naji komai da kuke fad'a,don haka a shirya nake muje mu nemo Bobby duk inda yake kafin ranar d'aurin aure yayi.


 Daga ranar ne muka shiga neman Hakeem ta koina inda sae yau Allah ya nuna muna shi zai shiga wani Hotel.
  Kinji abinda ya kasance pinky ba a riga an d'aura aure ba kuwa mun kawo miki Hakeem har gida kuma fasa auren da akayi a yau duk Naini ne ya sami dabara na ganin iyayen sa kar su iso yau, ko yanzu fitar nan da kika ga za'ayi abokanan sa ne wad'an da sukayi karatu tare a new Delhi suka matsa sae anyi Indian night, ba irin zillewar da bai yi musu ba amma suka nace shiyasa kika ji abun kai tsaye.
   Wani  irin farin ciki pinky ta qara tsintar kanta a ciki yayinda Feenah ta kawo qarshen zancen ta,billy ta kalli Naini inda ta shiga yi mishi godiya tare da nuna farin ciki kan namijin qoqarin da yayi.
   Nan yaji sauqi a ransa domin kalaman da ta mishi masu tausasa rai ne.
   Sai yaji gabad'aya ya haqura ba abinda yake fata irin ya sami mace irin ta wacce har ya fara tunanin ya same ta.

A hankali Billy ta miqar da Hakeem tsaye yayinda  Hakeem ya jingina a jikin ta tare da rungumo ta ya dora kan sa a kafada'ar ta sbd ko tsayuwa baya iya yi da kyau.
   D'ago kanta da zata yi ne taga ashe kaf mutane na zagaye dasu har su Abba,
 duqar da kanta tayi ba tare da tayi mamakin ganin su ba sbd ba wata tafiya mai nisa suka yi ba tasan wani  ne yaje ya sanar da su abinda ake ciki.
 a hankali ta d'ago fuskarta ta kalli Abban Hakeem tace"Abba don Allah kayi haquri kar kace zaka hana Hakeem shiga gida wlh ko kad'an baya da laifi nice silar komai abisa bahagiyar fahimta da na mishi.
   Abba yace ba komai mamanah sbd ke zan bawa Hakeem damar shiga gida kuma zamu so muji wannan shiri naku wanda ba mu riga mun fahimta ba.
  Na gode Abba amma zan so kayi haquri har muje gida inyaso acan sae  nayi bayanin komai.
  Ba komai mamanah dama a can ya dace ayi bayanin ba a nan ba don haka ku shiga mota muje gida ,nan suka shiga mota suna isa gida suka zarce main falo,
feenah ce taje ta kira umma,ya kasance Abban Billy, Abban Hakeem,umma ,Hakeem,Billy,Naini,and Feenah sune zaune a falon yayinda gurin yayi tsit ana sauraren abinda pinky zata ce.
   Duqar da kanta tayi qasa idanun ta suka ciko tap da qwallah muryar ta na rawa tace"Abba zan so kuyi haquri kan abinda zai fito daga bakina duk da cewa nasan dole zaku ji haushi na,a gaskiya wannan takardar sakin ba Hakeem ne ya rubuta ta ba nice na rubuta ta da hannun na kasancewar yaudarar Hakeem da nayi ya koya min rubutun sa sbd tun kafin muje new delhi nake tsara ganin na rabu da auren shi,bayan  munje ne bamu jima sosai ba na shiga nuna mai a zahiri komai ya wuce a gurina amma a bad'ini sam ba haka bane nayi haka ne don na samu na shawo kanshi domin ya fara sona sbd a ganina na idan muka rabu ba soyayyata a tare dashi sam ba zai ji zafin rabuwar mu ba, shiyasa na shiga yi mishi komai kamar da gaske wanda nasan sannu sannu abuwawan da nake mishi zasu sa ya fara sona.
  Da haka ne har ya fara sona kuwa wanda kan sona ne ya tashi sadaukar da ranshi da duk wani farin ciki nashi sbd  wani  al'amari da ya faru tsakani na da Naini,nan ta shiga yi musu bayani dalla dalla sannan ta ci gaba da cewa duk a tunani na plan ne suke shida doctor na ganin plan d'ina ya koma kaina ashe sam ba haka bane da gaske dai Hakeem ke sona.

 Kuma dalilin da yasa Hakeem yace shi ya rubuta saki ashe accident d'in da yayi yasa ya manta duk wasu abubuwañ da suka faru wata biyu da suka wuce, wanda naji haka ne a bakiñ Feenah lokacin da na shiga daki ina kuka kan auren da naji zaka hada ni da  Naini.

Da na shiga d'aki ina kuka nake sanar da ita nan ta share min hawaye inda ta kulle koina na d'akin bayan tace zata bani wata shawara wacce bata son kowa yaji.

A maimakon naji tace wani abu sae kawai naga ta fashe da kuka tace"pinky wlh naso na cutar da ke amma na sami kaina da kasawa duk da cewa cike nake da jin haushin ki kan na hanaki bada takardar saki amma kika qi,hakan yasa nace zan aure Hakeem domin na nuna miki kuskuren ki ba wai don ina son shi kad'ai ba,amma kuma sae na shiga tunanin a yanda na fahimci Hakeem yana sonki da kamar wuya ya kula wata 'ya mace,
 sae gashi bayan Hakeem yayi accident doctor ya sanar dani irin matsalar da Hakeem ya samu na ya manta komai da ya faru na wata biyu da suka wuce, wanda doctor ya fada min ne sbd ya dauka cewa ni er uwar Hakeem ce,
 da farko na shiga damuwa sae kuma nayi farin ciki da na tuna kenan Hakeem ya manta duk wata soyayya da yake yi miki,
 yanzu zan iya samun damar fara nuna mishi tawa soyayyar.
 Hakan yasa na roqi doctor kar ya sanar da kowa halin da ake ciki.
  Inda duk wani fad'a da Abba keyi kan sai Hakeem ya bar gida duk ina ji kamar na fadi gaskiya amma kuma wani  6angaren zuciya ta ya hana ni, kuma da ace Abba ya bawa Hakeem damar magana a wannan lokaci da tabbas zai fahimci matsalar da Hakeem ya samu.
 
Da dare naje asibiti domin na sami Hakeem na sanar da shi cewa yazo gidan mu ni zan bashi masauki,
 yayinda ni kuma zan sami damar fara nuna mai soyayya  har mukai ga yin aure,
 sae gashi ban tarar da shi ba,
 nayi baqin ciki sosai har dai da na karanta takardar da ya bari sae dai jin cewa yana mai sauraren afuwar Abba a ko yaushe nan na fahimci cewa kenan bazai yi nisa ba ma'ana zai tsayà a cikin garin nan,
Nan na qudura a raina zanje neman sa koma a ina ne domin na maida shi gidan mu da zama.
  Amma kuma a duk lokacin na fito zanje neman shi sae naji rashin kyautatawa ta sbd ba a kanki zan nemo shi ba a tawa buqatar ne,
 duk da nasan irin damuwar da kika shiga sosai akan rashin sa,
  Ba abinda ke fad'o min irin nifa qawar ki ce wacce muka taso tun muna yara da qaunar juna sam cutuwa bata dace nida ke ba,bana jin zan iya cutar da ke ko kad'an.
 
Wlh pinky zuwan da nayi a yau banzo da niyar komai ba sae  don na sanar da ke komai na kuma roqe ki gafara.

Nan muka ci kuka tamkar wad'an da akayi wa mutuwa na kuma yafewa Feenah domin bana jin zan iya riqe ta da komai, amma kuma na qara shiga nadama sbd na lalata duk wata soyayya da Hakeem keyi min ta gaskiya yanzu ni kad'ai ke fama da son shi ya manta tawa soyayyar.

 Feenah ce ta katse ni da cewa"pinky dama shawar da zan baki ita ce idan Abba ya kira ki kan zancen auren Naini ki nuna amincewar ki.... a rikice na kalle ta domin na firgita da jin zancen ta bcs ta ya zan amince a matsayi na na musulma nayi aure kan aure,tace"pinky akwai dalilin da yasa nace hakan na tabbatar idan kika sanar da su Abba qarya kika tsara musu Hakeem bai sake ki ba,
to kuwa kai tsaye ciwon Abban ki zai iya tashi sbd baqin ciki,
 kin ga na d'aya kece silar accident d'in Bobby har ya sami matsala,
 na biyu kece silar da yasa Abba yayi fushi dashi ya kore shi wanda har yanzu Abba yaqi haqura.
  Haka ne Feenah nima abinda nake tunani kenan sae dai gaskiya wannan tunanin naki kamar bai yi ba domin ina gudun amincewa auren Naini yaje yaja min matsala.... kar ki damu inshaAllah zan nemo Bobby kafin ma a fara zancen auren,,, haka kike gani feenah?haka nake gani domin yafi ace sae Bobby ya dawo ko zaki sanar da su Abba komai bcs ransu ba zai 6aci sosai ba,irin ace  Bobby baya nan.

Shike nan Feenah naji kuma Allah yasa ayi sa'a amma ya kike ganin Naini zai ji bayan an sanar da Naini auren mu daga baya yaji akwai auren Bobby a kaina?wannan ba matsala bane sbd shi musulmi ne duk kuwa cikakken musulmi yana da tawakkali kuma zai fahimci cewa dama ke ba rabon sa bace ,,, to Feenah Allah yasa ya fahimci haka,,,Amin ni zanje domin na fara aikin neman Hakeem daga yanzu.
  Nan na mata godiya ta fita.

Sae gashi har aka yi sati biyu ba wani  bayani har umma tazo min da zancen ansa lokacin aure hakan yasa na firgita sosai har ina qoqarin sanar da umma akwai auren Bobby akai na amma na fasa,
 nan na kira Feenah ta shiga kwantar min da hankali,wanda haka take min kullum har  yau da Allah yasa suka ga Bobby kuma ina tunanin matsalar da ya samu ta kau a bisa furucin da ya min lokacin da ya bud'e idon shi.
  Amma don Allah Abba kuyi haquri Ku yafe min wlh bada niya na aikata hakan ba,na tsorata ne da abin da Bobby zai sanar da ku domin na dauka cewa wani  sharri zai min,amma don Allah kuyi haquri.

Ba wanda yace komai cikin su domin sun cika da mamaki sae ajiyar zuciya suka sauke.
   Abban Hakeem kuwa damuwa ce  fal ta bayyana a fuskar sa  ya nisa yace"mamanah kema ina mai baki haquri sbd ya zama dole ki haqura da auren Hakeem sbd accident d'inda Hakeem yayi doctor ya sanar dani Hakeem ya sami matsala wacce ba zai ta6a iya biyan buqatar sa da mace ba bare zancen haifuwa.

Zumbur pinky ta miqe tana ji kamar ta kurma ihu,me yasa ta zamo silar jawa Hakeem wannan babbar matsala,kuka ta fashe da shi tana kallon Abban ta da umma  wad'an da suma da alama sae yanzu suka ji matsalar  domin sun shiga tashin hankali sosai.
  Taje cikin kuka  gurin Abban Hakeem ta durqusa kan guiwoyin ta tace"Abba don Allah kayi haquri kar a raba auren mu,wlh Allah zan iya zama da abuna haka koda kuwa ace bani ce sila ba bare nice sila.... Mamanah ai qaddara ce Allah ya riga ya rubutu hakan zai faru da Hakeem sae dai kiyi haquri domin ko a addinan ce baza a had'a mai lafiya da marar lafiya guri d'aya ba, shiyasa kika ji nace dole za a raba auren ku,
 kuma barin ki dashi cutuwa ce a gare ki.... wlh Abba zan iya zama da shi a haka,Abba yayi shiru cike da damuwa kuma da alama pinky ta bashi tausayi ganin yanda ta shiga rud'u,cikin muryar rarrashi yace "mamanah kiyi haquri kinji ba yanda zanyi duk da na fahimci kuna son junan ku amma dole Ku haqura da juna a bisa qaddarar da ta same ku"
      Kuka ta shiga yi sosai taje gurin Abban ta tana roqon shi kan yasa bakin shi ita zata iya zama da Bobby a haka.
  Kasa ce mata komai yayi domin ya cika da jin takaicin ta nan ta garzaya gurin umma tana roqon ta,
 umma kam kuka ke qoqarin zo mata shiyasa ta kasa cewa komai duk ta cika da tausayin d'an ta Hakeem,
ganin haka yasa pinky ta garzaya gurin Hakeem wanda idanuwan sa sun cika tap da qwalla magana take mishi amma ya kasa ce mata komai ya kafe guri daya sae kallon ta yake cike da tsananin so inda ya shiga tunanin yanda zai iya rayuwa ba ita.....cikin kuka ta girgiza shi tace Bobby kayi magana mana ka sanar da su ni mai iya rayuwa da kaine a ko wane hali kake ciki....pinky ni bazan so ki cutu ba dole muyi haquri da son da muke yiwa junan mu, nan ya fashe da kuka mai tsanani ya rungume ta a qirjinsa tace"don Allah Bobby kace ka amince zamu iya rayuwar mu a haka please kaji Bobby,,,d'agowa yayi yana mai share mata hawaye yace"i'm really sorry pinky,I'm really sorry sbd abinda kike so ba zai yiyu ba kuma ni mai son ki ne bazan so na tauye miki jin dad'in rayuwar ki ba,sae dai nace muyi haquri da junan mu kinji,,,,komai kasa ce mishi tayi sae kallon shi take hawaye na fita a idon ta kamar yadda shima Hakeem ke fitar da hawaye yayinda yake jin kamar ace mafarki yake ba gaske ba.
 
   

*Billy giro😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 7:51 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [8/27/2016]

*👛BILLY PINKY DURLING👛*




*Na*
   *Billy giro😊*




*page*

   *👛55👛*
A qirjin sa ta shiga kai mai duka mai kama da dukan shagaw6a tace"meyasa zaka ce haka Bobby bayan kasan baza mu iya rayuwa ba a tare ba,why Bobby?.
   Abban ta ne ya daka mata tsawa yace"kina da hankali meye haka! a tsorace ta tashi ta fad'a jikin Abban Hakeem wanda yazo domin hana Abbanta ya dake ta.
   Zama yayi da ita kan seater sae kuka take kan jikin sa shi kuma yana rarrashin ta.
    Hakeem kuwa duqar da kansa yayi yana mai kallon center carpet hawayen sa na d'iga akai.

Cike da tausayi Abban Billy ke kallon shi ya kalli Abban Hakeem Yace"yaya inaga wannan matsala abu ce da za'a iya magan ce ta,domin bai kamata abar Hakeem haka kawai ba,,, haka ne amma da kamar wuya har dai a yanda doctor yayi min bayani,gaskiya na karaya sosai da jin bayanin shiyasa na jima ina tunanin yanda zan sanar da ku wannan matsalar,,, yaya sanin kan ka ne ina da wani aboki a Germany qwararren likita ne a fanni wannan matsalar kuma inshaAllah zai iya magance ta,,,haka ne idan ance Allah ba a rashi amma yanzu ya kake ganin za'ayi? zan so nima kamin bayanin yanda doctor yayi ma bayanin matsalar in yaso na kira abokin nawa na sanar da shi idan yace Hakeem yaje sae yaje,to shiken nan zan sanar da kai bayan mun sallame su.
  Mamanah kukan ya isa haka tashi kije daga ciki kinji,to Abba amma ina so naji idan abokin Abba yace Bobby yaje, to shikenan jeki umman ku zata sanar da ke.
   Ba musu ta tashi haka Naini da Feenah suka tashi cike da tausayin Hakeem,yayinda kowanen su yaja motar shi suka fice.

Pinky kuwa daki ta nufa,tayi kwance  lamo  ba abinda take karantowa a zuciyar ta face addu'oin samun nasara har kusan 30 mnt tana abu d'aya,umma ce ta shigo d'akin ta zauna gab da pinky, yayinda
Pinky ta tashi tana mai share hawayen ta hade da duqar da kanta qasa domin yanzu cike take da jin nauyin umma,
umma ta dafa kafad'ar ta tace"Billy ki kwantar da hankalin ki domin abokin abbanki ya bawa Hakeem damar zuwa Germany ya same shi domin ya duba matsalar ko Allah zai sa ya magan ce ta,sae dai abbanku yace a tare zaku je sbd wani  dalili, yanzu ba abinda ya dace face ki ajiye kuka gefe ki rungumin addu'a domin ita ce magani,yanzu kije Hakeem baya jin dad'in jikin sa kuma da alama yana buqatar abinci sae ki samar masa wani  abun da zai ci.
  Nan umma taja hannun ta suka zo downstairs inda suka sami Amjad yana duba Hakeem,bayan ya gama en binciken sa ne ya kalli Abba yace"Abba Maganin bacci Hakeem yasha wanda yafi qarfin sa ma'ana yayi over dose shiyasa kwata kwata baya iya tsayin kirki har jiri na dibar sa.
   Hakeem ya duqar da kanshi ganin Abba nayi mishi kallon tuhuma kafin Abba yace komai Hakeem yace Abba kayi haquri ban sha don komai ba sae don rashin lafiyar da na kamu da ita sosai da ke hana min bacci.
  Ajiyar zuciya Abba ya sauke wandà har ya soma nadamar korar Hakeem daga gida sbd ya d'auka shaye  shaye ya fara.

  Duk da haka dai don Allah iyaye ku kula Ku riqa haquri kan duk abinda 'ya'yan ku suka muku kar kuce zaku Kore su daga gida,ku bisu da addu'a da kuma fatan shiriya domin korar su daga gida zai iya haifar da wata matsala wacce tafi matsalar da yasa kuka kore su.
  Allah dai ya bamu ikon kiyaye wa ya kuma bamu ikon haquri da 'ya'yan mu.
   Ya kuma sa 'ya'yan mu su kasance masu mana tarbiya da tausayin mu.
  Ameen.

Abba bai ce komai ba sae allura da amjad ya yi ma Hakeem ya kuma bashi magunguna.
  Ya fita tare da yi mishi Allah sauwaqe.

Bayan Amjad ya fita umma tace da Billy ki taimaka mishi yaje 6angaren shi sannan kizo ki samar masa abinda zai ci.
  Nan ta taimaka mishi suka je 6angaren shi.
  Ta dawo ta nemi ruwan tea sbd shi Hakeem yace zai sha.

Da ta koma ne ta same shi yana son ya tashi tsaye amma jiri bai bar shi ba da sauri ta ajiye flask d'in hannun ta taje ta kama shi suka zauna tace"Bobby me kake so?wanka nake son nayi pinky help me please,,,ok Bobby.
  Nan ta jawo towel ta zauna tana cire mai buttons din rigar shi bayan ta cire mai rigar ne ta taimaka mishi ya tashi tsaye,
 a hankali take zare mai belt d'in wadon shi inda tana aikin ne cike da jin kunya,ganin haka ya zare wandon da kanshi,ya zamo daga shi sae d'an guntun wando.

  Har toilet ta kai shi ta had'a mishi ruwan wanka ta fito.
  Ta d'auke tufafin da ya cire ta kai su inda ya dace.

Ya d'an jima kafin yake fitowa tayi saurin tarbo shi gudun kar ya fadi.

Sae da yayi shirin kwanciya sannan ya nemi ta had'a mishi tea.

Rungume yake a qirjin ta tana bashi tea cike da kulawa.
  Da ya gama ya kwanta  ta rufa mishi blanket.
  Tayi mishi sae da safe kafin take fita daga d'akin.
  A hankali Bobby ya tashi ya biyo bayan ta ba tare da ta sani ba,har tazo 6angaren su umma inda taji qofar gam,
  tsaye tayi tana tunanin danna door bell....no ki bar su kawai muje a nawa 6angaren kiyi bacci, a tsorace ta juya ganin hakeem yasa ta sauke ajiyar zuciya tace"Bobby Allah har kasa naji tsoro"
  Am sorry na rakoki ne sbd gidan nan yana da fad'in da yasa bazan iya barin ki kizo ke kad'ai ba.
   Thank u Bobby amma bai kamata ace ka taso ba a halin da kake ciki, ai na daina jin jiri qarfin jiki ya rage.
  Zo muje ki kwanta naga kamar bacci kike ji sosai,
 bai jira me zata ce ba yaja hannun ta suka je 6angaren shi.
 
Rungume yake da ita wacce tuni tayi bacci shi kuwa sae kallon ta yake ganin yanda take motsi,motsin da ya kasa gane dalilin yinsa.
 

Pinky kuwa kayan da ke jikin ta ne suka dame ta,wacce da alama gigin bacci ya mantar da ita d'akin da take nan ta shiga kiciniyar cire rigar jikin ta amma ta kasa sbd bayan ta a daure yake, kukan shagwa6a ta shiga yi tana ta jan rigar, a hankali ya kai kunnen sa a bakin ta yace"oh pinky stop craying lemmi remove it to you"
  kamar a mafarki take jin maganar domin har yanzu bata farka ba.
    A hankali ya zare mata zaren rigar ya cire rigar ya barta da Bz sannan ya cire mata skirt,wani wando ne a jikin ta na kayan d'an guntun iya cinya,bai cire wandon ba ya barta da shi, ya rufa mata blanket sannan ya tashi ya dauke kayan da ya cire mata ya kai su inda ya dace koda ya dawo  ta yaye blanket d'in da ya rufa mata  ta tashi zaune ido rufe tana qoqarin cire bz.
  Nan Hakeem ya hau gadon ya jawota jikin sa yana kiran sunan ta a hankali yace"me kike shirin yi ne pinky ita kadai ce a jikin ki fa.
   Da sauri ta saki ma6allar Bz ta jawo blanket ta rufe qirjinta  tace"Bobby bana iya bacci da bz"
ok ina zuwa,
 nan ya dauko mata wata er qaramar T shirt.
  Taje toilet ta cire bz ta saka rigar ta dawo ta kwanta.
   Shima Hakeem kwanciya yayi tare da jawota jikin sa suka lula duniyar bacci.


*Billy giro😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 7:53 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [8/28/2016]

*👛BILLY PINKY DURLING👛*




*Na*

*Billy giro😊*


 *page*
      *👛56&57👛*
Da asuba Hakeem ne ya fara tashi ya kalli Pinky yanda ta shige qirjin sa sosai kamar wacce zata sha mamma.
   Pinky kuwa sanyi ne ya dame ta sosai sbd anyi ruwan sama cikin dare ga kuma sanyin Ac.
     A hankali yake yaye blanket d'in jikin su wanda dama kad'an ya rage ya sa6ule a jikin su.
     Pinky ta qara dunqule qafafun ta cikin muryar bacci mai hade da shagwa6a tace"please Bobby ka rufa min Blanket ina jin sanyi sosai"
  Asuba tayi pinky u have to wakeup kinji.
    Cike da natsuwa take yunqurin ta shi sae dae da alama ko kad'an baccin bai ishe ta ba.
      Shima tashi yayi ya kashe Ac had'e da kunna na'urar da zata d'ima ma musu d'akin.
   A bedside ya zauna close to pinky ta jingina a jikin sa tana murza idonta tace"uhm uhm Bobby"
mene ne pinky? bacci bai ishen ba,,, yi haquri bari kiyi sallah sae ki koma kwanciya kinji.
  Ba musu ta miqe tana miqa a hankali Hakeem kuwa yaje ya d'auko mata sabon brush ya bata.
   Bata wani  jima sosai ba gudun kar ta
 6ata mishi lokaci har aje a tashi sallah.
 
 Tana fitowa yaje yayi arwala ya fito ya nemi jallabiya ya saka pinky tace"Bobby jikin naka yayi sauqi?naji sauqi pinky..but Bobby har yanzu fa naji jikin ka da zafi,,,naji sauqi kar ki damu kinji,
  Ya fad'i haka ne yayinda ya shafi gefen fuskar ta sannan yace "am sorry pls ki nemi wani  abu kiyi sallah bana so na rasa jam'i da na nemo miki kafin na fita".
  Um um Bobby ni bazan yi sallah anan ba,
 zan bika mu fita tare nasan yanzu an bude 6angaren mu.
   Shiru yayi domin ji yayi ana yayyafi amma kuma baya son takura ta nan ya nemo jacket mai hula ya saka mata ya d'auko  lema ya ja hannun ta suka fito yakai  ta har 6angaren su umma ta shiga sannan ya fice masallaci cikin sauri.

  Tana shiga ta nemi hijabin sallahn ta mai rufe mata jiki shif har qasa ta saka,
 bayan ta gama sallah da minti biyar ta kwanta sbd baccin da take ji sosai.
 
Guraren qarfe goma Hakeem ya shigo gidan ya sami gwaggo mai aiki tana jera abinci kan dining.
  Umma ce ta qaraso gurin ta tace"kin kammala ko akwai saura kinga har Hakeem ya shigo,,
ai na kammala komai, to gwaggo sannu da qoqari kema je kici naki abinci.

  Kafin ta bar gurin sae da Hakeem ya qaraso ya gaisa da su.
  Hakeem yace"umma jiya mantawa kukayi ku ka rufe 6angaren ku with out pinky? No Hakeem Abbanku ne yace a barta kawai ta kwana a can sbd rashin lafiyar da kake fama da ita,,,
amma ya naga bangan ku a tare ba?
Ai tun da Asuba na rako ta ta dawo,,,ok je ka duba idan ba bacci take ba se tazo muyi break fast.


Koda Hakeem ya shiga ya same ta sae bacci take sanye da jacket din da yasa mata,,,
 ta wani  rungume teddy sosai a qirjin ta.
   Zuwa yayi gab da ita ya yaye mata sumar kanta da ta rufe mata fuska.
sannan ya sauke ajiyar zuciya a hankali ya fita daga d'akin.

Yaje ya sami umma da Abba zaune kan dining suna jiran su.
  Sae da ya gaisa da Abba ya nemi guri ya zauna,
 Abba yace"ya jikin naka?Alhmdlh naji sauqi.
  Umma tace ina"Billy ko bata tashi bane? eh umma.
  Daga haka sukayi shiru umma ta zuba musu abinci suka fara ci.

Bayan sun gama ne Abba zai fita yace da Hakeem"yaushe ne kake ganin zaku je Germany? ko gobe ma iya zuwa Abba, ok but kubar tafiyar zuwa jibi dai dai kun kammala komai na tafiyar.

  Hakeem Yace"to"kafin Abba ke fita.

 zaune Hakeem yake shida umma suna kallo sae dai hankalin sa baya ga  kallon ganin har sha biyu tayi pinky bata fito taci abiñci ba.
   Cikin natsuwa ya kalli umma yace"umma wai har yanzu pinky taqi ta fito fa,,, Hakeem Billy ta jima bata sami baccin kirki ba shiyasa kaga na bar ta,amma ya kamata ace ta fito haka, kaje ka tashe ta.
   Bai riga ya tashi ba sae ido ya daga yana kallon qofar pinky a hankali yaga qofar ta bude pinky ta fito,tufafin jikin ta yake kallo er fincikar riga hakan yasa tayi saurin komawa ta canzo zuwa doguwar riga.
 
Tana qarasowa gurin shi ta sake mishi murmushi, lumshe idon sa yayi d'auke da murmushi a fuskar shi yana kallo taje ta kwanta jikin umma tana mata ina kwana.
   Umma tace aike za'a yiwa ina kwana kin shige d'aki kina ta bacci tun dazu,
kallon umma tayi a shagw6e tace"Allah umma baccin bai ma ishe ni ba yunwa ce ta tashe ni.
   Ai ga break fast d'in ki can tuni yake jiran ki.
   ta fad'i haka ne yayinda ta tashi ta bar gurin acewar ta gaji da zaman kallo zata je ta huta.
  Pinky kuwa d'an gidan ta quaker oats taje kan dining ta had'o ta zo kusa da Hakeem ta zauna,kallon da yake mata ne yasa tace "zaka sha"
 ta fad'i haka ne yayinda ta debo spoon ta kai a bakin sa.
  Half of spoon yasha ya kar6i spoon d'in ya bata rabin ta shanye yace" kinji yanda yayi zaqi sosai ko?
  Bobby kaine dai baka son zaqi amma dai dai yake.
   Bai ce mata komai ba sae matsawa da yayi kusa da ita ya kar6i cup din oats ya shiga bata har sae da tace ya ishe ta, goge mata bakin ta yake da tissue yayinda yake cewa"oya je ki debo plantain ki qara akai,
no Bobby ciki na ya cika sosai har ma ji nake kamar zai fashe"Hakeem yayi fari da ido yana kallon ta yakai  hannun sa kan cikin ta yace wannan cikin ne ya cika da yawa har kamar zai fashe?
  Cike da dariya tayi saurin jaye hannun shi sbd yanda yake lallatsa cikin da yatsan sa,,,,
 ta kwantar da kanta kan kafadar shi ta rirriqe hannun shi sae dariya take tana fad'in ka daina Bobby zaka sani amai fa,Allah cikina baya nuna na qoshi da yawa please stop it Bobby😂.

Duk abin nan da suke umma na upstairs tana hango su inda ta sami kanta cikin farin ciki yau ga Hakeem da Billy zaune guri d'aya har suna wasa da juna.

Murmushi tayi had'e da girgiza kanta ta koma daga ciki.


Bayan kwana d'aya.

Yauce ranar da zasu je Germany Hakeem ya shigo cikin gidan sanye da riga mai dogon hañnu baby pink
 in colour,
 da baqin wando yayi matuqar kyau sosai sae qamshi ke tashi a jikin sa.

Cike da natsuwa yaje ya durqusa ya gaida umma da Abba da ke zaune a falo sun amsa gaisuwar cikin farin ciki ganin kalar rigar Hakeem da ke sanye a jikin sa.

Umma tace jeka daga ciki ka sami Billy kar ta 6ata muku lokaci.
  Ba musu ya tashi ya haura sama.

 umma ta kalli Abban Hakeem tace"Alhmdlh mun gode Allah,Allah dai ya bawa Hakeem lafiya domin muci gaba da ganin su a haka,
  "Amin" cewar Abba.


Hakeem na shiga ya sami pinky ta shirya tsaf cikin riga da wando baby pink in colour,
 tayi rolling da gyale kalar kayan,
 tayi kyau sosai, tana ganin shi tayi tsaye cikin mamaki tana qare mishi kallo ya wani hard'e hannayen sa a qirji tace"wow Bobby ka ga yanda kayi kyau a cikin kalar nan kuwa? girgiza kanshi yayi cikin murmushi yace"um um sae kin fad'a, tace "ok zo na gaya ma"
 ta fadi haka ne yayinda ta ware hannayen ta.
  Hakeem yaje a hankali ya fad'a kan qirjin ta, ta kama kunnen shi ta rad'a mai cewa"Allah Bobby yau kayi min kyau sosai har ina ji kamar na saka ka a jaka ta na 6oye,, meyasa? turo baki tayi tace"to so kake wata ta ganka ta qyasa ne,kiss ya d'ora mata a bakin yace
"ai ba wacce ta isa ke kad'ai ce tawa kuma ni kad'ai ne naki, don haka bazan bar kowane namiji yaga wannan kyakkyawan dressing ba.
   Ya fad'i haka ne yayinda ya d'auko black after dress wacce ya gani kan bed ya saka mata,ta fito sak kamar balarabiya.
  Ta d'auki hand bag suka fito.


A hankali ta qarasa gurin su umma ta gaida su,
sannan taje da murnar ta gurin Abbanta wanda shigowar sa kenan.

 kiss ta d'ora mishi tace "sannu da zuwa Abba"
 yauwa mamanah har kun shirya.
  Eh Abba"ta fadi haka ne yayinda ya gaisa da su umma sannan ya zauna ya fuskanci Hakeem da kyau yace"Hakeem abinda nake so da ku shine  idan kunje bada shan magani kad'ai zaka dogara ba, ku d'ora da yin istigifari sosai ba dare ba rana idan kukayi haka inshaAllah baza ku dawo qasar nan ba sae kana mai cikakkiyar lafiya,,,
inshaAllah zamu kiyaye hakan Abba,
 maganar ta fito a bakin Hakeem da Pinky,
 Abba ya kalli Billy yace"ji bakin ta kamar da gaske"
 cike da jin kunya ta 6oye fuskar ta a qirjin sa tace"Allah Abba da gaske nake"
 To Allah yasa
amin Abba.

Nan suka tashi inda su Abba suka raka su,suka shiga mota sae bye bye suke musu kafin suke fita gidan, yayinda su Abba keyi musu fatan nasara.



Satin su uku a Germany Hakeem ya samu kulawa sosai a gurin Abokin Abban pinky domin a gidan shi ya basu masauki ga matar shi mai matuqar son mutane ce,
 hakan yasa Billy taji dad'in zama garin wanda a ko yaushe tana cikin waya da su umma da Feenah.
   Kuma kamar yadda Abban Billy ya gaya musu basu yi wasa da hakan ba domin ko yaushe cikin yin istigifari suke, kamar yadda su Abba suke taya su haka Feenah da Naini.

    My fans mu riqe hakan duk wanda keda wata matsala ya maida istigifari abun yi kuma haniqam ba dare ba rana,inshaAllah Allah zai yaye ma matsalar idan buqata ce ita ma inshaAllah Allah zai biya ma.
   Amma sae mun sa haquri da kuma fatan nasara a ko yaushe.
   Allah dai yasa mu dace Amin.

Yauce ranar da suka dawo Nigeria su duka biyu sunyi er qiba wacce ta qara bayyanar da kyaun su.

Bayan sunci abinci sunyi wanka sun huta,pinky na d'akin umma sae fira suke.
   Shigowar Hakeem ne ya katse su ya sami guri ya zauna.
  Umma ta kalle shi cike da kulawa tace Alhmdlh Hakeem tun kuna can munji ka sami lafiya inace ka sami tabbacin lafiyar ka a gun matar ka ko?duqar da kanshi yayi yace"tukuna umma"meyasa ko kuma nace meye amfanin zuwan Billy ba don ka sami tabbacin lafiyar ka bane kafin ku dawo?
shiru yayi domin shi kanshi yaso hakan amma tsananin tsoron da Billy ke yiwa abun ne yasa ya haqura ya barta,
Umma tace "tambayar ka nake Hakeem"
d'ago kanshi yayi yana  kallon  Billy, tayi saurin kauda idonta.
  Umma ta lura dasu inda ta fahimci wani  abu,ta kalli Billy cike da natsuwa tace"Billy be wise mana mijinki ne fa ya kamata ki barshi domin ya sami tabbacin samun lafiyar sa kinji,
 kunya Billy taji kamar ta nutse cikin qasa har ta kasa cewa umma komai,
Umma tace"yanzu sae ki tashi kuje 6angaren shi kafin gobe ku tare part d'in ku.
  Tana gama fad'a ta fita sbd taji qararrawa alamar Abba na son ganin ta.

Tana fita Billy ta d'auki d'an qaramin pillow ta jefowa Hakeem tace"wai meyasa baka jin kunya shine kuna magana da umma ka wani  kallo ni.
 Ta fad'i haka ne yayinda ta murgud'a mishi baki tana harararshi da wasa.
  Pillown ya dauka yayi kamar zai jefa mata shi da qarfi,
 har sai da ta tsora ta tayi saurin rufe fuskar ta da tafukan hannyen ta,tace"wayyo umma!
 a maimakon taji saukar pillow sae taji saukar kiss"ta bude fuskar ta a hankali tana kallon shi yace"tashi muje kin dai ji abinda umma tace saura kuma kimin kuka na ko tsotse bakin tas har sae ya qara laushi,cike da alamar zata yi kuka ta maqale kafad'a tace"please Bobby ka tausaya min,,zan tausaya miki fiye ma da yanda kike tunani kinji just lets go to d bed my dear.
  Nan yaja hannun ta suka fita sae kukan shagwa6a take mishi.


*Billy giro😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 8:02 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [8/28/2016]

*👛BILLY PINKY DURLING👛*




*Na Billy giro😊*


*Page*

   *👛58&59👛*
Sun kawo matakalar sauka taqi yarda su sauka sae komawa bayan shi tayi tana mishi kuka, murmushi yayi ya d'auke ta cak yace
 "so kike ki tara mana jama'a ko".
  Ya fadi haka ne yayinda ya shiga da ita d'akin ta ya ajiye ta kan bed yace
"ai ko a nan zan iya domin na fahimci kafin mu qarasa 6angare na sae kowa ya gama jin mu".
  Nan yakai  hannu ya kashe wutar d'akin  ya shiga zare hannun rigar ta a hankali wanda da qyar ya samu ya cire rigar sbd yanda ta riqe rigar gam sae kuka take duk jikin ta ya d'auki rawa kan wasar da yake tayi da qirjinta,
 bai kula ta ba,
 yaci gaba da sha'anin shi wanda yayi 15mnt akanta,jin da gaske kukan ta ya wuce na shagwa6a yasa ya kunna wutar d'akin tayi saurin sa hannu ta kare qirjin ta,
Kafin take lalubo rigar da ya cire mata,ta kare qirjin ta da ita, ta kuma yi saurin sauka kan gadon ta nufi gun wardrobe ta tsaya tana kallon Hakeem da ya qaraso gurin ta yana mata wani  kallo mai cike da sha'awa,
 ta wani  kame a jikin wardrobe qirjin ta na kai komo sbd numfashin da take a tsorace,A hankali Hakeem ya matsa gab da ita tare da kai hannu yana son jaye rigar da ta kare qirjin ta da ita,hakan ya gagare shi sbd yanda ta riqe rigar gam tana girgiza mishi kai cike da hawaye a idon ta,,nan ya saki rigar,
 yakai  bakin sa kan nata kamar wanda zai sa harshen sa a ciki sae kuma ya fasa sbd jin sautin kukan ta ya qaru,rungume ta yayi a qirjin sa yana bubbuga bayan ta,
yakai  bakin sa a kunnen ta yana magana a hankali"
Pinky meyasa ko romance ba kya bari muyi duk kibi ki tsorace,bafa abinda zan miki da wasa nake kuma ki daina kukan nan don Allah yana azabtar dani sosai kinji,
Ya fadi hakane yayinda ya d'ago ta yana
share mata hawaye, nan ta sauke ajiyar zuciya ta koma kan qirjin sa ta kwanta,tana jin yanda yake fitar da numfashi sai duk taji ya bata tausayi tace"pls Bobby kayi haquri nima ban san meyasa nake jin tsoro da yawa haka ba.
   Dan guntun murmushi ya bayyana a fuskar sa yace"don't worry"
  Sannan ya bud'e wardrobe  ya d'auko mata tufafi,yakai  hannu zai zare rigar qirjin ta,ta riqe gam tace"ina zamu je ne Bobby?dama  Feenah zamu je d'aukowa motar ta lallace kan hanyar zuwa gidan nan,
ki juya bayan ki idan ba kya so na ganki ina so zan saka miki riga,
 ba musu ta juya a hankali,ta saki rigar hannun ta,
 ya saka mata rigar da ya d'auko ,
yana cikin rufe mata zip suka ji  sallama had'e da knocking,Hakeem ya amsa sallamar yayinda ya juya da pinky yana qara share mata hawaye sannan ya kalli Feenah wacce ta shigo ta riqe qugu tana kallon su tace"iyyeh yanzu ma kuke shirin zuwa d'auko ni kenan.
   "Sorry Feenah"
Ba komai Bobby kaje Amjad da Naini na jiran ka a falo.


Nan ya fita daga d'akin Feenah ta kalli Billy wacce ta shiga gyaran gadon ta da ya
 yamutse sannan ta cire doguwar riga ta maida kayan bacci.
  Feenah ta cire mayafin ta taja hannun pinky suka zauna,tace"lafiya keda Bobby duk naga jikin ku  a sanyaye kuma da alama kuka kikayi bcs naga kamar yana share miki hawaye,kallon ta kawai pinky tayi tace"nidai me ya kawo ki da daren nan haka? Nazo taya amarya bacci ne...wace amaryar?ke mana ko Bobby bai gaya miki irin qasaitaccen bikin da za'ayi a gobe kafin ku tare part d'in ku?um um bai gaya min ba,,, inaga surprise yaso baki,,,qila haka ne but yaushe ne bikin naki keda Naini... ke pinky yaushe ne muka fara soyayyar?......duk fa wayar da nake dake a Germany kuna a tare tamkar kun jima kuna soyayya da juna.....shin wai yaushe ne ma kuka fara soyayyar?,,, hmm tun lokacin da muka fara neman Bobby yake d'an nuna min ni kuma ina nuna mishi kamar ban gane ba har dai yazo ya nuna min gabadaya bayan tafiyar ku Germany,
 ban wani  ja mishi rai sosai ba sbd nima na kamu da son abuna sbd tausayin da ya bani kan rasa ki da yayi,,,
gaskiya kun dace sosai Feenah sae dai nace Allah ya sanya Alhairi.
  Amin.

Daga haka suka kashe wutar d'akin suka shiga bacci.


Washe gari  duk en uwan su Billy dake garin mai duguri suka iso,haka abokanan umma duk sun zo kamar yanda 6angaren Hakeem abokanan sa na qasar waje suma suka zo,har da doctorn new Delhi da kuma iyayen Naini.
 

Pinky kuwa zaune take ana zana mata lallai fatarta ta qara ja da haske sae sheqi take wanda da gani tasha gyara,
  Sae kallon yanda gidan ya cika maqil take wanda abin har mamaki yake bata yaushe ne akayi gayyace2 nan haka duk bata sani ba wanda taron har yana son yafi na bikin  auren su.

Bata gama shiga mamaki ba sae da taga hatta abokan su wad'an da sukayi primary, secondary,high school kaf ba wanda Feenah bata gayyata ba,sosai pinky tayi farin ciki domin ta jima bata had'u da wasu ba.

Gidan yasha kwalliya pink and white haka mutane white & pink colour ce a jikin su,sae kid'an taushi ke tashi ana jiran fitowar amarya da Ango.

Hakeem ne keta faman kutsawa cikin mutane da qyar ya samu ya shiga d'akin pinky ya same shi maqil da abokanan ta.
   Suna ganin shi se kowa ya fita d'akin, pinky ta juyo tana kallon Hakeem yayi matuqar kyau wanda rabon da ta ganshi tun daren jiya.

Cikin natsuwa ta qaraso gurin shi ya sake mata lallusan murmushi yace ya haka kina son 6ata mana lokaci bayan kinsan event uku za'ayi a yau, duqar da kanta tayi tace"rigar ce bata yi min ba zip din yaqi rufuwa.
  Yace juya muga"
 nan ya gwada qoqarin shi amma zip din bai rufu ba yace ashe dai matata tana da er qibar ta ban sani ba na bada qaramin size,murmushi tayi tace"to yanzu ya kenan?kin sanya bz? Eh,,, ok go n remove it.
  Nan taje toilet corner ta cire ta dawo, yana rufe mata rigar sae ko zip din ya rufe, yace"juyo muga idan ban takura abokanan wasa ta sosai ba, ya fadi haka ne yayinda ya juyo ta yana mai kallon qirjin ta, kunya Billy taji ta rungumo shi kad'an tace"nidai Bobby kallon ya isa haka,,, naji qarasa shirin mu tafi bata wani  6ata lokaci ba ta gama shirin suka fita.
 
Suna isa aka fara kid'e kid'e wanda ko a kwance  kake sae ka raya bare a zaune,ai kuwa nan mutane naga kowa sae tashi suke suna raya wa kafin daga bisani aka ci gaba da yin komai cikin tsari,yayinda naira tasha kashi garin kari kyace sune mallakin CBN lol😉

Tsananin kyaun da sukayi ne yasa duk inda suka shiga en camera sea binsu suke suna daukar su hoto ba ko qaqqautawa,haka kowa sae fitar da  wayar shi yake yana  d'aukar su hoto,yayinda Hakeem ya maqale Billy a jikin sa sae murmushi yake wanda kallo d'aya zaka yi mishi kasan yana cikin farin cikin da bai ta6a shiga irin sa ba,haka ma Billy.

An jima sosai ana shagali sannan aka dakata kowa ya yafi zuwa sallah aka sake wani  wanka cikin kayan sojowa,haka kwalliyar gidan aka canza ta zuwa kalar uniform d'in sojawa,Billy tayi matuqar kyau cikin kayan sojawa sbd sunyi d'as a jikin ta,yayinda abokanan ta suka kasance hular soja da farar riga da wandon soja haka Abokanan Hakeem,
Se ya kasance Hakeem da Billy kad'ai ke cikin complete  uniform,tafiya suke sojawa securities na biye dasu,
 zasu je gurin zaman su da aka ke6e wanda yasha ado da komai na kalar sojawa gurin yayi matuqar kyau kyace shugaban sojawan duniya ne zai hallari gurin,suna isa gurin basu riga sun zauna ba naji an tashi busa wacce nake sa ran ta sojawa ce sae naga kowa ya tashi tsaye suka qame kyace statue.
     Ogan Hakeem ne ya iso gurin d'auke da kyaututtuka ya miqa ma Hakeem da Billy, Hakeem ya kar6a yayinda ya sare ma ogan,
 suka d'an russunar da kansu shida pinky alamar godiya.

  Da haka aka ci gaba da aiwatar da bikin yanda ya kamata.

Sae zuwa yamma aka sake wani  shirin domin qasaitacciyar walimar da za'ayi inda aka gayyato shaharraren malami yayi wa'azi mai matuqar amfani ga duk wanda ya saurare shi musamman matan aure.


Guraren qarfe goma na dare duk wata hud'uba da duk wani  abu da za'ayi wa amarya anyi sae qoqarin kaita part din ta ake.

Hakeem ne riqe da hannun ta suka fito yayinda motaci ke jere a harabar gidan nan naga kowa ya shiga mota,aka tashi motacin inda ake je cikin gari aka yo rally aka dawo,ba'a zarce koina ba sae 6angaren su Hakeem 6angaren ya qayatu cikin white n pink colour gidan yayi bala'in kyau komai a tsare kamar gidan turawa,duk da pinky cikin mayafi take amma tayi matuqar farin cikin ganin yanda Hakeem ya tsara musu gidan komai choice d'in ta.

Bayan kowa ya watse Hakeem ya matsa gab da pinky tare da yaye mata mayafi yana kallon kyakkyawar fuskar ta wanda tasa ya sauke ajiyar zuciya ya saki murmushi jin dad'i ita ma pinky murmushin ta mishi,hannun ta yaja suka je toilet basu fito ba sae da sukayi arwala, sannan sukayi sallah raka'a biyu suka godewa Allah da yasa suka zamo ma'aurata.
 Bayan sun gama ya ciyadda ita tamkar yanda ango ke ciyar da amaryar sa cike da nishad'i,haka ita ma ta ciyadda shi, sae da ya kasance cikin kowanen su yayi dam sannan suka tashi sukayi brush.

Kwance  yake har yayi shirin kwanciya yana kallon pinky wacce ita ma tayi shirin kwanciya sae neman wani  abu take a cikin wardrobe duk yabi ya qagu ta hau gado sbd shi kad'ai yasan abinda yake ji.

Pinky kuwa ba abinda take nema face tana fargabar hawa gadon shiyasa tayi kamar mai neman wani  abu domin ta fahimci tun d'azu Hakeem ke mata wani  kallo wanda ya bata tabbacin yau komai zillewar ta ba zai barta ba.

Hakeem Kam kasa haquri yayi ya taso yazo gab da ita ya rungumo ta ta baya yana shinshinar qamshin jikin ta,daga nan ya sunkuce ta sae kan bed ya kashe wutar d'akin ya qara manna ta a qirjin sa inda yakai  hannu kan fuskar ta yana shafa ta a hankali.



*Billy giro😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 8:06 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [8/30/2016]

 *👛BILLY PINKY DURLING👛*




*Na Billy giro😊*


*page*
 
   *👛60👛*
Haka ya ci gaba da tafiyar da al'amurran sa komai a natse, cikin hikima da dabara yake lalla6a pinky har ya samu ya raba ta da kayan jikin ta,nan tafiyar ta canza zuwa wani salo mai cike da qwarewa wanda shi kanshi ya sami kansa yana aiwatar da hakan ne, duk yabi ya rikice yana aika mata saqonni ta koina,pinky najin yanda yake sarrafa ta ta koina ba abinda take face numfashi da kuma qoqarin ganin bata yi kuka ba,hakan yasa Hakeem yaji dad'i sosai yaci gaba da tafiyar da al'amuran sa,cikin natsuwa ya shiga yin addu'ar saduwa da iyali inda pinky taji baqon al'amari yana shigar ta a hankali amma duk da haka sae da taji wani  zafin bala'i wanda yasa ta fara kuka ba shiri sae roqon Hakeem take amma tuni hankalin sa ya gushe domin yauce ranar farko da ya tsinci kanshi a irin wannan duniyar ta ma'aurata.
   Ba irin kukan da pinky bata yi ba kan ya barta amma jin kukan yake kamar a mafarki,aikinsa yake ba kama hannun yaro yayinda kukan ta ke qara masa qarfi,
 bai barta ba sae da yaji he is totally satisfied.
  Wani  irin farin ciki Hakeem ya tsinci kanshi wanda ji yake kamar aljanna ce aka tsunduma shi.
  Hamdala yayi wa ubangiji ya jawo pinky a qirjin sa sae lallashin ta yake cike da son tayi shiru.
   Amma pinky kukan sae abinda ya qaru yayinda take yarfi da hannu tana kiran umma da Abba,,,
 sae duk Hakeem ya shiga damuwa ya rasa me zai mata domin tayi shiru, can ya lumshe idon shi a hankali ya had'e bakin sa da nata ya kai  d'ayan hannun shi yana wasa da dukiyar fulanin ta,tare da qara shigar da ita a jikin sa yana qoqarin sake second round, a rikice pinky ta zare bakin ta daga nashi hawaye sha6e sha6e ta had'e tafukan hannyen ta tana magana cikin muryar kuka wacce har ta disashe tace"uhm uhm please Bobby na roqe ka don Allah kar ka sake"
mugun tausayin ta yaji duk da cewa ba da gaske yake zai yi second round ba, yace"to ki daina kuka idan ba kya so na sake kinji"ta gyad'a kanta cikin sauri tace"Allah na daina"nan ya share mata hawaye ya kwantar da ita a qirjin sa,yana mata wani  abu wanda yasa ta fara jin sauqi ta kuma ji dad'in hakan shiyasa ta qara lafewa sae shafar qirjin sa take a hankali yayinda baccin sauke gajiya ke son fizgar ta,nan ta rufe  idanunta a hankali.

   Hakeem ya kalle ta cikin kulawa yana gyara mata sumar kanta da ta yamutse  yayinda tausayin ta ke qara fizgar shi yace"Billyta"
  Bata d'ago ta kalle shi ba sae idanun ta da ta bud'e a hankali yace"muje muyi wanka tukun kinji"
 Bata ce da shi komai ba sae daukar ta yayi suka je toilet, shi ya mata wankan da kanshi ya saka ta cikin ruwan zafi zai gasa mata jikinta sae kukan shagwa6a take mishi tana son fita cikin ruwan,
shi kuma yana faman lalla6a ta kamar qwai har ya samu suka kammala wankan suka fito.

 zaunar da ita yayi kan stool yaje ya canza zanin gado ya saka tufafi ita ma ya d'auko mata rigar bacci sae dai koda ya juyo yaga ashe ta d'ora kanta jikin mirror bacci yayi awon gaba da ita,,
"Allah sarki pinky"
  shine abinda ya furta yaje a hankali ya dauke ta ya kwantar kan bed  ya mayar da rigar da ya dauko domin baya son takura ta,nan shima ya kwanta ya jawota ta jikin sa yana jin yanda take sauke numfashi a hankali da haka har bacci ya kwashe shi.


Da Asuba shine ya fara farkawa, ya jima yana kallon pinky kafin yake zare jikin sa a hankali yaje ya shiga toilet.
    Koda ya fito sae motsi take ta lalubo teddy ta rungume.
Yazo gab da ita ya zauna yace"pinky asuba tayi yi haquri ki tashi muyi sallah kinji"
   Ba musu ta yunqura ta tashi zaune tana tunanin yanda zata ji idan tayi tafiya,Hakeem ya lura da hakan yace"muje na kaiki toilet? girgiza kanta tayi,,
yace "zaki iya tafiya kuwa?
cikin sanyin murya tace zan iya.
  Yace"ok je kiyi arwala kizo muyi sallah ko"
  Nan ta gyara d'aurin towel d'in ta ta tashi ta shiga toilet.
  Hakeem sae kallon ta yake inda ya fahimci ta jure ne kawai.

Bayan sun gama sallah basu riga sun tashi kan darduma ba Hakeem ya jawo pinky jikin shi yana mata sannu,,,bata ce mishi komai ba sae hannunsa ta d'ora kan cikin ta tace"Bobby yunwa"me kike son ci? My favourite,
  Olryt ina zuwa kinji,
 ya fadi haka ne tare da d'auko mata pillow ta kwanta sannan ya fita,
 bai jima ba ya dawo dauke da Quaker oats.

Bayan ya gama bata ne suka koma kan bed suka shiga bacci.



Sae guraren qarfe tara Hakeem ya tashi yayinda Billy ta qara gyara kwanciyar ta alamar ci gaba da bacci.
 Bai zare jikin sa ba sae da ya d'auko teddy ya saka mata tare da dora mata peck a goshi.


Wanka yaje yayi ya shirya cikin tufafin da suka kar6e shi sae qamshi yake,
 yaje downstairs ya zauna falo yana kallon labarai.

Ya jima a zaune bcs har 11 tayi nan yaji qarar bud'e qofa sannu sannu.
  D'aga kanshi yayi ya hango pinky ce ta fito cikin shiri mai kyau English waers riga da skirt wad'an da basu nuna tsiraici kuma sukayi matuqar d'aukar ta.

Tana had'a ido dashi tayi saurin duqar da kanta cikin jin kunya ta kuma yi tsaye har sae da  yazo ya d'auke ta,sae kallon ta yake cike da so long time har sae da taji kunya ta 6oye fuskar ta a qirjin sa domin ba abinda take tunawa kamar abinda ya faru tsakanin su a daren jiya.

Shidai Hakeem murmushi kawai yayi sannan ya sauka da ita downstairs suka zauna kan seater,ya kalle ta da kulawa yace"Billyta hope da sauqi gurin ya daina miki zafi sosai ko?shiru kawai tayi ta riqo hannuñ shi tana wasa da yatsun sa,can ta d'ago ta kalle shi kamar wacce ke son yin kuka.


*Billy giro😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 8:08 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [7:45AM, 8/31/2016]

 *👛BILLY PINKY DURLING👛*





 *Na Billy giro😊*



*Page*
 
 *👛61👛*
Tace"Bobby wai har yanzu su Feenah basu shigo bane? Pinky ke nake jira sae kin tashi daga bacci tukun ko zan bud'e 6angaren,amma yanzu tunda kin tashi bari naje na bud'e,,,
Bobby zan bika,,,ok muje,,, ya fad'i haka ne tare da riqo hannun ta suka fita.
  Suna isa qofa suka ji knocking koda Hakeem ya bud'e Baraka ce mai aikin pinky riqe da basket na abinci sae da ta gaida su sannan tace"umma tace a kawo wanda tun d'azu aka kammala break fast d'in sae aka sami 6angaren ku a rufe kuma tayi kiran number ka a kashe,,, mtsw haka ne fa na manta da wayar na a kashe since yesterday but yanzu je ki jera mana abincin kan dining.

Suna dawowa Hakeem yaje ya d'auko wayar shi ya kira umma da suka gaisa take cewa"wane irin bacci ne kuke tayi haka Hakeem, bayan kasan mafi yawa har dai abokanan ka yau suke son komawa kuma ya kamata su kanga kafin su tafi amma kaje ka shantaqe kana ta bacci,,, umma yi haquri Allah tun d'azu na tashi but na manta cewa ban kunna waya ta ba,,,to shi kenan yanzu kuyi ku gama break fast abokanan Billy da mutanen Maiduguri suna son shigowa kafin su fice,,, ok umma nan ya ajiye wayar, ya jawo pinky suka fara break fast.

Basu jima da kammalawa ba mutanen Maiduguri suka shigo tare da su Feenah,shi kuma Hakeem ya tafi old 6angaren shi inda ya bawa abokanan shi masauki ya samu tuni umma tasa an kai musu break fast sunci.



Billy cike da fara'a ta gaisa da en uwansu na maidugiri tana wasa da en qananan 'ya'yansu.

Sun jima suna fira a falon yayinda Billy tasa Baraka ta kawo musu abubuwan  motsa baki.


Feenah taja Billy suka je d'aki tace
 "ke wannan tafiyar fa sumui sumui kamar wacce bata son motsa jiki,,,da wasa ta dalla wa Feenah harara tace"dama ya nake tafiya? a hankali kike tafiya amma hankalin tafiyar yau yayi yawa,,, au shi hankali har yawa yake?eh gashi na gani a gunki yau... kingan ki Feenah Allah sa idon ki yayi yawa but zan miki ubanshi ne idan kika yi aure, gwara ma ni na jure har ina game cinyoyi na ina tafiya,ke nasan a yanda kike son jiki sae dae na same ki a kwance  ba kya ma iya motsin kirki...cab ai wlh kin fini son jiki...naji nidai meyasa kika taso ni ina zaman zama na ko don kawai kiga tafiya ta ne?a'a wlh kayan jikin ki zaki canza kin wani  sanya mana English wears sae kace ba Amarya ba,,, oh oh Feenah ta kura ni kawai kike so kiyi, wlh ni ban cika son sa hausawan kayan nan ba fa kin sani nauyi suke min...kar ki damu akwai wani  material da na gani mai bala'in kyau a cikin akwatinan lefen ki Allah baya da nauyi ko kad'an gashi ya sami d'inki mai kyau ba wani  rigima a d'inkin,nan Feenah ta d'auko kayan.

  Ba a son rai Billy  ta saka kayan ba amma tayi matuqar kyau fiye da kayan da ta cire.
   Feenah tayi tsaye tana qare mata kallo  tace"wlh Allah kinyi kyau sosai har dai d'aurin d'ankwalin nan har mamaki ki ban wai kece kika d'aura shi bayan ba kya saka iren iren kayan nan,,, ah ah kaji ki don bana saka kayan sae na kasa sarrafa kaina yanda naso ko kuma da nike ganin kuna d'aurawa fa....oh sorry na manta cewa ke gifted ce kallo d'aya zaki yiwa abu ki riqe bare ma kin sha ganin munayi,,,,
dalla mata harara tayi tace "Feenah bana son zolaya fa".... Hmm ba wani ai kin san gaskiya na fad'a....mtsw kinga zo muje don Allah kin san na bar mutane a falo kuma sunce suna so zamuyi photo kafin su tafi,,,nan suka fita.

Da zuhur mutanen maiduguri suka wuce,su Feenah da sauran abokanan Billy kuwa suka shiga kiciniyar had'awa abokan Hakeem abinci sbd sun fasa komawa sae gobe da safe.


Da dare kowa ya watse Hakeem yaje 6angaren su umma ya tafi d'akin umma yana fad'in wai umma ina pinky ta shiga ne tun lokacin da mukayi break fast ban sake sata a idona ba sae qawayen ta nake ta gani suna zirga zirga kuma yanzu kowa ya watse bata 6angaren mu,,,,,Ayyah ai Billy tunda en Maiduguri suka wuce wani irin zazza6i ya taso mata tun sannan tana kwance sae idan anyi sallah take tashi tayi,,,cike da damuwa ya kai duban shi gun Billy wacce sai yanzu ya ganta qundundune cikin blanket sae rawar d'ari take,,,ta6a jikin ta yayi yaji yayi mugun zafi shiru yayi cike da damuwa komai ya kasa cewa sae zama yayi tare da yaye hular kanshi had'e da yin guntun tsaki,,, umma tace"lafiya? umma inaga tun ciwon kai da zazza6in da ta fara a Germany ne yake bin ta har yanzu,sbd taqi bari ayi mata allura bare zazzabin ya tafi gabad'aya,,,,,ai yau da kukan ta da komai nasa aka mata allura kuma na tasa ta gaba taci abinci tasha magunguna shine ta d'an samu bacci ya d'auke ta amma kuma sae rawar d'ari take,,, to umma ko zan bar ta  nan ne taci gaba da baccin ta har safe?a kan me ka dai tashe ta ku tafi 6angaren ku,,, ko kad'an bai so hakan ba sbd baya son ya tashe ta daga bacci kuma yana jin kunyar daukar ta a gaban umma,haka ya tashe ta ba a son ransa ba yaja hannun ta suka wuce.

Tana shiga d'aki ta cire skirt d'in jikinta sannan ta zuge zip d'in rigarta bata iya cire rigar ba ta fad'a ruf da ciki kan bed sbd taji tsayuwa na son gagarar ta shiyasa ma ta kasa jiran Hakeem da ya tsaya rufe musu 6angaren su,,,,Hakeem ne ya shigo bai zarce koina ba sai gurin ta ya zauna ita ma ya zaunar da ita tare da jingina ta a jikin sa yana qarasa cire mata rigar,ya zamo inner wears ne a jikin ta,a hankali yakai  hannun sa kan ma6allar bz bai cire mata ba sae da ya d'auko towel,,,yace"muje na miki wanka bata iya ce mishi komai ba sae towel ta kar6a ta kare qirjin ta tare da qara lafewa a jikin sa,shafo gefen fuskar ta yayi cike da damuwa yace"pinky wai kodai zafin abun ne ya sa ki zazza6i? murya qasa qasa tace"um um its headache kuma allurar da aka min har yanzu gurin na min zafi,,ta qarasa maganar cikin muryar kuka yayinda take share hawaye tace"kuma sae da nace ma umma bana son allura amma tasa aka min,,, yi haquri ya isa daina kuka kinji, bari na murza miki gun,nan ya kai hannun sa a bayan ta yana murxa mata gurin da aka mata allura sannu sannu,
tun tana fad'in wash wash tana riqe mishi hannu har ta daina tayi shiru daga haka tayi bacci.
   A hankali Hakeem ya d'ago fuskarta yana kallo yaga alamar baccin na mata dad'i,ganin ta fara zufa  kuma zafin jikin ya fara sauka.

Ya kwantar da ita ya samo qaramin towel da ruwa yana daddanna mata fuskar ta  har zuwa qirjinta wanda hakan yasa ta sauke ajiyar zuciya a hankali,bai barta haka ba sae da ya nemo riga ya saka mata suka shiga bacci.

Da safe guraren 8 Hakeem ne ya fito daga wanka riqe da d'an qaramin towel yana goge ruwan jikin sa,Billy ya samu tana shafa jikin teddy a hankali yace"Billyta har kin tashi? d'ago idon ta tayi, tayi saurin rufe su sbd komai babu a jikin sa,hakan yasa ya koma toilet corner ya d'auro towel ya dawo,damuwa ce fal ta bayyana a fuskar shi sbd fuskar ta ya shafo yaji zafin jikin ba sauqi,riqo hannun shi tayi ta bud'e idon ta a hankali tana kallon shi.


*Billy giro😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 8:15 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [3/9/2016]

*👛BILLY  PINKY  DURLING 👛*



*Na  Billy giro😊*


*page*

     *👛64&65👛*
Kwance suke suna  dubin  silin yayinda  suka  lullu6a da  blanket  Wanda  ya  Kai  har  ixuwa  qirjinsu,kowanen  su  na  dauke  da dan murmushi  a fuskar sa musamman  Hakeem Wanda ya  qara  jawo  pinky  a jikin shi ya  bata  peck  a kumatu tare  da  dauke kansu  photo  Pinky ta kalli photon tace  "gaskiya  photon  nan  yayi  kyau" ta  fadi  haka  ne  yayinda ta shafo gefen  fuskar  shi tare da  dora  hancin  ta  a  kan  nashi kamar wacce  zata dora  mishi  kiss  kan  lips
sae kawai ya sake dauke  su photo
 bugo  qirjin  sa  tayi tare da kar6e wayar tace  "wai Bobby  meye haka?hancin ta  yaja  yace" bani  waya ta ko Kuma yanxu hancin nan ya  qara  tsayi
 bata bashi ba  sae  qoqarin  goge photon  take
da sauri yace"no  kar  ki goge min photo fa.
  Dangwara mishi wayar  tayi  a hanun sa  da ya miqo  ta  bashi  ta  juya  mishi  baya ya kalli  photon  yaga  sunyi  bala in  kyau har  ma yafi  na farko
murmushi  yayi  ya  kalli  pinky  wacce  ta  juya tana  fishi  da  shi  yace "baki  san  kyau kike qara  min  ba  idan  kina  fishi kalli wannan  photon  kiga
 A  hankali  ta  juya tana  kallon  photon  wani  murmushi  ne  ya  su6uce mata ta shiga mamaki sbd photo ne  wanda  tun  suna  new  delhi   lokacin  da  yasa  ta  wankin  mota  ruwa  suka  jiqa  ta  ta wani  turo  baki a shagwa6e tana  kallon  qafar  wandon  ta,
 ajiyar zuciya ya sauke yace "tun  a lokacin  na fara jin  wani  abu a  game  da  ke har  na  fara  jin  ina  son childish  behavior naki" murmushi tayi yayinda  yake  ci  gaba  da  nuna  mata duk fotunan da  ya  dauke  ta  tana  mishi  wankin  mota ba tare da  ta  sani ba
kuma duk sae tayi matuqar kyau ya  kalle  ta  da kulawa yace "kin san  me  pinky?um  um sae ka  fad'a
 Allah ina sonki
  Cikin  jin  dadi  ta  rugumoshi a  hankali ta dora mishi  kiss  a kumatu tace "luv  u  more my soldier man "
 Rungume  ta  yayi  sosai  a qirjin  sa ya shiga yaye blanket  din  jikin  su  a hankali
bata  hana  shi  ba  duk  da  tasan  ba  komai a  jikin  su
 tsure  qirjin ta  yayi da  kallo  cike  da sha'awar ganin sa bcs  bai ta6a ganin  qirjin  ta  cikin  haske sosai ba se  yau

ajiyar zuciya ya  sauke ya kalli pinky  wacce  taja  blanket  ta  rufe qirjin  ta,
nan ya lumshe idon shi a hankali ya hade  fuskokin  su guri  daya sea yawo  yake  da  harshen  shi  kan lips  din ta yayinda ya  zira hannun sa cikin blanket kan qirjin  ta yana yawo da shi slowly slowly nan  ya hade  bakin su guri daya suka  dauki  lokaci
 cikin  hikima  pinky  ke zare  jikinta sbd  ganin  yanda Hakeem ke  son  fita  hayyacin sa.
  Kallon ta yayi yace "pinky me  ne  ne? kasan  lokacin sallah  ya  kusa  ya  kamata muje muyi  wanka
ta fadi  haka ne  yayinda  ta  bashi  towel ya  daura  ita ma haka.
 goya  ta  yayi zasu tafi toilet  sae  kid'a  take a bayan  shi tana rawa da kai tana rera waqa" ni nawa d'an masoyi yana sona har goya ni ma ya keyi muje toilet gaba tsundum baya tsundum a aljanna "
murmushi  yayi  hade da  girgiza  kan  shi yace" kin  raina  ni  ko zan  sauke  ki  fa saurin  dainawa tayi tare da  kwantawa  a bayan shi ta lafe  sosai tace yi haquri kar  ka  sauke  ni Allah  ina  jin nishadi sosai idan  ka  goya  ni .... sbd me? sbd bayan ka  yana da dadin kwanciya ta fadi  haka ne yayinda  suka  shiga  toilet.

Bayan  sun  fito  sun  shirya Hakeem ya wuce  masallaci Koda ya dawo tayi sallah ta gyara  dakin  tsaf  sae qamshi ke tashi.
  Tace"Bobby pls ina so xanga sabuwar moto ta"
 ba musu  yaja hannun  ta  suka  fita  harabar gidan yana yaye rigar  motor ta  daka  tsalle ta  qanqame  shi tace "wayyo Allah Bobby! wlh wannan  motor ta  hadu  ko  a  mafarki  ban  ta ta6a ganin irin ta ba woohuu muah!
 ta dorawa  motar  kiss sannan  ta  juyo  ga  Hakeem ta bashi hot kiss sae qara gode mishi take kafin take  marairaice  fuska tace" please Bobby zo muje yawo mu d'ana motor.... Zuwa ina pinky ? ko  zuwa gidan su umma ne
ya nuna  gidan yace nan gidan na kusa da mu? eh ina  so xan  nuna  musu  motar
 ok naji je ki shiryo daga nan sae muje gidan su Abba (cewa da Abbanta) tace"Allah? yace "Allah kuwa ....yeah ta tafi da gudu ta shiryo suka shiga motor suka je ta nunawa  su Abba sae murna suke taya ta daga nan suka wuce gidan Abban pinky
 Cike da murna mahaifin su ya tarbe su haka  matar  shi Hajiya seema inda pinky sae mamakin murnar matar take domin tasan ko kadan yanzu matar bata son ta, shiyasa sam  bata shiga sabgar ta.
   Suna  gama gaisawa tasa aka kawo musu abinci da abin sha sae fara'a take musu suna fira Abban Billy duk yaji dadi a ransa ganin yanda matar shi ta sake da Billy ba Kamar ko yaushe ba har ya tuna da rayuwar su ta da .
    Wayar Hajiya seema ce tayi qara ta tashi ta haura sama zuwa daki ta d'aga wayar tace yauwa kamar kinsan ina son kiran ki,yanzu Billy tazo kuma Kamar yadda kika bani shawara na fara nuna mata hakan yanzu so nake ki aiko min wannan pills din da mukayi magana akai but inace  yana da qarfi Kamar yadda nake buqata.....ke kuwa sau nawa zan gaya miki cewa yana da qarfi sosai wanda kan qarfin sa yasha lalatawa mata mahaifa har sae da companyn maganin suka dakatar da sayadda shi aka hana shan sa ma gabadaya sae da suka qera wani sabon sanfari.
    Tabbas kin gaya min haka har ma kikace a sati sati ake shan sa but ni a kullum zance ta riqa shan shi in yaso naji labarin lalacewar mahaifar ta nan take.
  Dariya sukayi a tare sannan tace ki aiko min fa yanzu ina jira tace"to"kafin suke ajiye waya.
 
Sun jima a gidan inda
Billy taji dadin zama gidan sbd yanda matar Abban ta ta sake mata shiyasa ma ta nemi Hakeem da ya barta ta  yini a nan.

Sae dare Hakeem yazo d'aukar ta inda Hajiya seema ta bawa Billy turarukka masu qamshin dadi na larabawa,sannan tace "ina zuwa"
nan ta haura sama zuwa daki ta dauko maganin da qawar ta ta aiko mata pills cikin wata er qaramar kwalba nan ta dauko wata empty kwalba hade da kwalin ta wanda kwalin kallo daya zaka yi mishi kasan maganin mata ne.
  Juye pills din tayi ta saka cikin empty kwalbar ta rufe ta saka ta a cikin kwalin ta.
 Ta fito cikin sauri yayinda fuskar ta ke duke da murmushi tace "kinsan yanzu maza sai da hakan" nan tayi mata bayani tace "kuma ba abu ne da zaki bari Hakeem yasan da shi ba then every night zaki riqa shan shi kar ki tsallake ko wace rana .
Da murmushin jin kunya ta kar6i maganin tayi mata godiya ta tafi da sauri sbd Hakeem da ke faman jiran ta a mota.
   Koda taje ta same shi ya kada sit din mota ya kwanta idanun sa a lumshe sae waya yake yana dariya en yatsun ta biyu ta kai ta lotsa su cikin dimples din shi tace"my soldier man da wa kake waya haka sae faman dariya kake?sae da ya tsinke wayar yace "nida Amjad ne wai sae kin maida ni mijin Hajiya just bcs ba a jima da bikin tarewa ba amma har kinsa mun fara fita......kae kae shi Amjad ya fad'i haka shida komai yiwa matar sa yake kuma duk abinda take so shi yake mata kullum yana biye da ita kamar wani bita zai zai  but inace baka yarda da zancen  sa  ba dai ko? na yarda mana gashi kin bar ni tun dazu sae faman jiran ki nake kamar wani drevan hajiya
yayi maganar ne kamar wani qaramin yaro har sae da abin ya bata dariya ta kama kunnen ta         tace "to yi haquri my little soldier man bazan sake ba kaji am baba" murmushi kawai yayi yaja motar suka fice suna ta faman dariya kan wani labari da yake bata.

Suna zuwa suka fada wanka sukayi shirin bacci inda sukayi kwance kan bed suna kallon wani film ana gama film din Billy tayi bacci nan Hakeem ya kashe Tv ya kuma rage hasken dakin tare da gyara musu kwanciya
 
Har sunyi nisa da bacci Billy ta tashi firfigit ta zare jikin ta a hankali taje ta bude jakarta ta dauko maganin da hajiya seema ta bata tasha.
Tana juyo wa ta hada ido da Hakeem yace"Billyta me naga kina sha kamar magani? Uhm eh maganin ciwon kai ne bcs ina dan jin kaina na min ciwo kuma bana son ciwon ya yawaita kace sae amin allura,,,
eyyah sannu  zo naji idan jikin naki bai yi zafi ba
 Nan ta hau gadon ta kwanta ya ta6a goshin ta har zuwa qirjin ta yaji ba wani zafi ajiyar zuciya ya sauke yace "kenan da sauki sosai? gyada mishi kai tayi cike da rashin jin dadin qaryar da ta mishi nan ya rungume ta suka koma bacci


*Billy giro😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 8:17 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [9/5, 10:21 PM] Billy giro😊:

*👛BILLY PINKY DURLING 👛*






 *Na Billy giro 😊*



*Page*

 *👛67&68👛*
Wayar sa ce tayi qara bai qaraso ba ya fita dakin nan tayi saurin shan maganin tana gama sha sae gashi ya sake shigowa ba shiri tasa qafa ta take pills din da bata riga ta tsince ba ta kuma yi surin 6oye kwalbar da ke hannun ta.
  Hakeem ya qaraso yayi tsaye yana kallon ta ita kuma sae faman tura qafar ta take a hankali tana tura pills under bed yayinda take kallon fuskar shi dauke da guntun murmushi yace "meyasa kika baro daki ko a nan kike so muyi bacci yau? um um
  To lafiya me yake damun qafar ki naga kin kasa tsaidata guri d'aya ko wani abu ya cije ki? ba komai
bai kula ta ba sae zaunar da ita yayi kan bed wanda hakan yasa ta tura kwalbar under pillow shi kuma ya durqusa ya dora qafar ta kan jikin sa yana duba qafar kafin yace wani abu ya hango pills qwara d'aya sae dai duk ya rarratse kan takin da pinky ta mishi.
 Dauko pills din yayi yana kallon ta yace "Billyta wannan maganin fa na mene ne?shiru ta mishi, ya tsure maganin da kallo ko zai gane wani abu,
cikin kakkausar murya yace" am asking u! uhm uhm...... ba kuka na tambaye ki ba so nake naji wane irin magani ne bcs bana so na miki rashin fahimta kallon shi kawai take
 idanun ta har sun cika da qwalla kauda fuskar shi yayi yayinda idanun shi suka kai gun jakarta da ke kan drawer wani irin kallo ya mata sbd kwalin maganin da ya zaro cikin jakarta,
da mamaki yace"pinky me kike yi da wannan magani? girgiza kanta ta shiga yi ba tare da tace komai ba yace "say something pinky stop doing dis talk to me" Bobby ba nawa bane.... na waye kuma ina kwalbar maganin take? nima ban sani ba.... kinga gaya min ina kwalbar take bana son qarya fa ! shiru ta mishi yayi2 da ita tayi magana taqi sae kuka take mishi, ransa ne yayi mugun 6aci ya daka mata uwar tsawa har sai da ta miqe a tsorace nan ya fizgi hannun ta suka  tafi d'akin shi suna shiga dakin ya saki hannun ta yaje ya kwanta zuwa tayi ta kwanta kan jikin shi tana mishi kuka tana bashi haquri tsawa ya daka mata kan ta sauka kan jikin sa qanqame shi tayi ta cusa fuskar ta a qirjin shi duk ta rikice tana bashi haquri  sbd ta dauka ko dukan ta zai yi, komai bai sake ce mata ba sae kukan ta yake saurare mai qona mishi rai tsaki yayi yace "wai baza ki sauka kan jikina bane ,
  Jiki sanyaye ta sauka ta tafi nesa dashi ta kwanta sae ci gaba take da kuka.
Rigar jikin sa ya kalla yaga duk ta jiqa gaban rigar da hawaye canza rigar yayi ya kwanta tare da juya mata baya.

  Dare yayi sosai amma kowanen su ya kasa bacci kan 6acin rai da kuma  sabon da sukayi wa juna na bacci manne da juna,
can Billy ta kwatanci Hakeem yayi bacci ta lalla6o a hankali ta kwanta bayan shi tare da rungumo shi.
  Hakeem da bai riga yayi bacci ba ya bude idonshi a hankali yana kallon hannayen ta da ta saqado kan qirjin sa shiru yayi abinshi har sae da yaji tayi bacci nan ya juyo yana kallon fuskar ta ya kai hannun sa a hankali yana share mata en hawayen da ya gani kan fuskar ta sannan ya qara rungume ta hade da sauke ajiyar zuciya yana shafa bayan ta a hankali daga nan bacci ya d'auke shi.

Washe gari ta riga shi farkawa ta zare jikinta a hankali tana kallon shi nan ya bude idon shi yana kallon ta tayi saurin kauda fuskar ta kamar mai jin kunya ta tashi ta bar d'akin.

Guraren qarfe goma yaje dakin ta ya samu tana toilet zama yayi kan bed ya dauki kwalin magani yana juya shi a hankali yana cikin haka ne yaji fitowar pinky a natse ya dago yana kallonta sanye da towel iya cinya kanta qasa yace"pinky zo ki zauna "a sanyaye taje ta zauna nesa da shi yace matso kusa zamuyi magana ne, ba musu ta matsa kusa da shi yace"pinky me yasa kike shan maganin nan kuma yaushe kika fara shan sa? 3days a go,
a wane dalili kika fara shan sa ko wata matsala na gaya miki kina d'auke da ita ko kika ga alamar hakan ? ko daya... to meyasa kike shan sa, shiru tayi yace" kar ki sake min shiru idan ina tambayar ki abu bana so, yi haquri, naji amma bani kwalbar maganin sbd bana so ki sake shan sa bcs Allah yayi min ke mai cikakkiyara ni'ma na kuma yi alfahari da hakan sosai don haka bana buqatar kina shan wani magani kinji, kayi haquri nima bani shi akayi ba wai ra'ayi na bane....dama nayi tunanin hakan but waya baki maganin? kayi haquri bazan iya sanar da kai ba, olryt bani maganin,
ba musu ta dauko maganin ta bashi ya kalle ta yace "pinky ina so kimin alqawari baza ki sake shan maganin nan ba" nayi ma alqawari bazan sake shan sa ba, maimata min naji, Bobby nayi ma alqawari bazan sake shan wannan maganin ba,promise? yes i promise to u, but idan kika sake wane irin hukunci zan miki?kamin komai ma, yauwa Billyta ai nasan ma baza ki sake sha ba ko? gyada mishi kai tayi yace "aha to mu tafa,da murmushi ta bashi hannu  suka tafa yace" then give me a kiss"
 ya fadi haka ne yayinda ya nuna kumatun shi Billy taje a hankali ta mishi kiss kan kowane kunce, murmushi ne ya bayyana a fuskar shi shima ya dora mata kiss a ko wane kunce ya kuma dora mata kan goshin ta sannan ya  je kan lips dinta ya dora mata, murmushi tayi cike da jin dadi ya jawo ta ya rungume yace " Billyta kiyi haquri da fushin da nayi da ke dama haka rayuwar aure take sae da haquri kinji" nima kayi haquri Bobby bazan so na sake 6ata maka rai ba "olryt tashi ki shirya muje muyi breakfast bcs yunwa nake ji,
tace" to " kafin yake tashi ya fita daga dakin ita kuma ta tashi ta shirya taje sukayi breakfast cike da nishad'i.

 Bayan sun gama su kaje 6angaren su umma sun jima sosai a can sae fira suke da umma,
Billy kam biye kawai take da su yayinda take faman jure ciwon da marar ta ke mata wanda tun jiya take jin tana mintsila mata amma ta basar.
   Hakeem ya lura da ita nan yaja ta suka koma 6angaren su, suna isa ta fashe mai da kuka yace " mene ne pinky? marata ke min ciyo sosai, dama kina ciwon mara ne? um um ban ta6a ba, to ya isa yi shiru zata daina ne may be canjin yanayi ne nan ya shiga rarrashin ta tun tana jurewa har ta fara mishi ihu tana fad'in wayyo Allah Bobby na shiga uku zan mutu don Allah ka taimaka min!  gabad'aya ya shiga damuwa sae shafa qasan cikin ta yake yana fadin "tayi shiru ta daina kuka zai daina amma ina kamar qara mata ake sae kuka take yayinda ko yatsan ta bata son motsawa kan bala'in ciwon da take ji nan ta riqe mai hannun da yake shafa mata gun sae kuka take ba wasa hawaye sha6e2 duk tayi zufa ta jigata cikin qanqanin lokaci .
  Tashi yake sonyi amma ta rirriqe shi tana fad'in "Bobby in ka tafi zan mutu don Allah ka tsaya " komai kasa cewa yayi duk jikin sa yayi sanyi ganin irin yanda take kuka cike da tausayi, nan ya samu da qyar ta saki hannun shi ya tashi zai je 6angaren su umma, wani irin
ihu ta saki ta fara juyi tana kiran sunan shi da saurin sa ya dawo yaga rigar jikin ta tayi staining da jini.
 Durqusawa yayi tare da tallabota jikin sa cikin muryar rarrashi yace "pinky yi haquri daina kuka kinji kinga ashe ma menstruation preod dinki ne yazo yana baki wahala, yarfi take da hannu tace" Bobby bai ta6a min haka ba don Allah muje asibiti ka duba kaga wlh Bleeding nakeyi sosai kamar fanfo a rikice Hakeem ya duba hankalin sa ne yayi mugun tashi ganin yanda take bleeding.....sallamar Amjad yaji yayi saurin amsa sallamar,
Amjad na shigowa yace "subhanallah Bobby me yake faruwa da pinky? ba wannan ba Amjad nidai muje asibiti nan suka fita hankali tashe sae asibiti.
Da qyar aka samu ta rage Bleeding inda har yanzu tana fama da ciwon mara sae dai ya rage ba Kamar farko ba hakan yasa akayi admitting din ta a aminity.

Jingine take a qirjin Hakeem shi kuma yana zaune yayinda hannunsa ke cikin rigarta yana shafa qasan cikin ta a hankali yana mata sannu hannunta ta d'ora kan na Hakeem tare da 'qara lafewa kan qirjin sa sbd baccin da ta soma ji kan allurar bacci da aka mata nan Hakeem ya zaro wayar shi zai kira umma sae ga Amjad ya shigo yace dashi kaxo zamuyi magana.
 Cikin kulawa Hakeem ya kwantar da pinky wacce har yanzu bata iya motsin kirki.

Yana shiga office din Amjad ya samu guri ya zauna yana mai kallon Amjad wanda yayi baqiqirin da rai, Hakeem yace "lafiya Amjad? Mtsw wai kai Hakeem yaushe ne zaka san ka girma ka daina biye wa son zuciyar ka kan baqar aqidar turawa gashi yanzu  kaje ka jawa pinky matsala tana Bleeding wanda har ma fargaba nake idan bata sami matsala ba ...... Amjad bangane ba me kake nufi ..... Ina fa zaka gane kaje ka durawa er mutane pills tana sha......zumbur Hakeem ya miqe tare da ture kujerar da yake zaune ta tafi sae shillo take tana juyi yace "pills! ita pinky? Sosai kuwa shine yayi causing din komai ba wai period time din ta bane but kar ka ce min baka san tana shan shi ba?wlh ban sani ba Amjad kawai dai wani magani nasan na kar6e a hannun ta wanda yake min kama da pills but ganin kwalin shi yasa na cire zargin pills ne yanzu haka yana a mota ta bara ma na dauko maka shi kaga,
nan ya tafi cikin sauri ya dauko ya kawo mishi koda Amjad ya duba yace "ya salam pills ne a ciki ba asalin maganin ba fa kuma ko pills  had'ararren pills wanda kan had'ararrin sa ne aka daina aiki dashi gabadaya at all ma an daina bugoshi,
Innalillahi na shiga uku wlh matsala yake kawo wa mahaifa a nan take a ina ta same shi Bobby ? bar ni kawai Amjad ina zuwa nan ya kar6i pills d'in ya fita rai 6ace yaje ya sami pinky wacce bata riga tayi bacci ba sae fama take da ciwon mara.
   Tana ganin yanayin Hakeem ta yunqura da qyar ta tashi zaune kafin yake zama,
cikin damuwa ta d'ora hannayen ta kan kumatun shi tana kallon qwayar idon sa da ta cika tap da qwallah nan kawai taji nata idanun sun ciko tace "what's wrong Bobby? sauke hannyen ta yayi ya zuba mata pills a tafin hannun ta yace" cin amanar da zaki min kenan ki hana 'ya' ya na zowa a lokacin da ya kamata,,as how Bobby nida ba Allah ba ta yaya zan hana 'ya' yan mu zowa a lokacin da ya kamata ........wane irin magani ne na zuba miki tukun ? Maganin da ka hana ni sha kuma wlh ban sake sha ba..... ban saki rantsuwa ba kawai ina son naji confirm shine kike sha kafin na hana ki ? Eh.....kina sane kenan da cewa pills ne kike sha!shiyasa kika canza kwalba acewar wani magani ne ba pills ba!
saurin kallon pills din tayi dake xube cikin tafin hannun ta tace "pills kuma ya haka?..... tsaki ya buga ya kalle ta cike da tsana yayinda hawaye suka gangaro kan kumatun shi yayi saurin share hawayen zai fita tace"Bobby don Allah ka tsaya wlh bansan pills bane trust me .....never! tace" never trust me? ta fadi hakane yayinda take kallon shi da mamaki a hankali ta taso a daddafe tazo har inda yake tace "please Bobby muje mu zauna na maka bayani kasan na gaya ma bani shi aka yi kuma ba kowa bace face...... Shiiii ban nemi jin wane bayani daga gare  ba don haka bazan 6ata lokaci na na saurari wani bayani a bakin ki ba!matsalar da kika ja mana kawai ta ishe ni!don haka ki barni naji da ita!
nan ya sauke yatsan sa da ya d'ora kan lips d'in ta ya fita daga d'akin.

Cikin kuka pinky ta tsure pills din da kallo hawaye na d'iga akai.


*Billy giro 😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 8:19 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [9/6, 10:24 PM] Billy Giro: [06/9/2016] Billy giro😊


*👛BILLY PINKY DURLING 👛*




*Na Billy giro 😊*


*Page*
     *👛69&70👛*
 Nan ta durqushe a hankali tana ci gaba da kuka.
  Amjad ne ya shigo ya same ta tace "Amjad wlh Allah ban san pills bane na gaya ma Bobby bai yarda da hakan ba"
  Ajiyar zuciya ya sauke yace "pinky to ya akayi hakan ta kasance ? nima  bansani ba  bcs ba siya nayi ba bani aka yi shine nake so na yiwa Bobby bayani yaqi ya surare ni please ka kaini gurin shi na samu ko zai saurare ni, pinky Hakeem ya fita daga asibitin nan,eh
nasan ba zai je koina ba face gida please muje ka kaini..... no pinky barin asibitin nan ba naki bane har sae anyi bincike kan mahaifar ki idan ba wata matsala sannan ko zaki iya tafiya..... no ni bazan iya ba Bobby yana fushi dani bana jin zan iya samun natsuwar komai har sai na shawo kanshi please Amjad kar ka ce a'a don Allah ka taimaka min... shike nan naji tashi muje,
nan ta lalla6a ta tashi suka tafi yana ajiye ta gida yace
"don Allah pinky ki qoqarta kiga kun dawo asibiti da wuri Allah bana so aje a sami matsala yanzu ina sauri ne kan wani patient da aka ce an kawo emergency"
InshaAllah Amjad.

Nan yaja motar sa ya tafi ita kuma ta shiga daga ciki koda ta murd'a qofar d'akin Hakeem ya rufe da key nan tayi ta danna door bell har ta gaji bai bud'e ba sbd yaga lokacin da Amjad ya sauke ta.
  Falo ta dawo ta kwanta bacci ke son fizgar ta amma taqi yarda da hakan sae jiran fitowar Hakeem take.
    Ta jima a kwance amma ba alamar fitowar Hakeem.

umma ce ta shigo gidan da sallama pinky ta amsa sallamar cikin muryar kuka.
   Cikin damuwa tace "lafiya me yake faruwa da ku ne Hakeem ya kirani kuma daji shima kuka yake yace naje asibiti na same ki naje ban same ki ba yanzu gashi nazo na same ki sae faman kuka kike ina Hakeem d'in yake ne ? umma yana daga ciki yaqi ya bud'e qofa.

  Nan umma ta tashi taje tana knocking tana mishi magana ba musu ya bude qofar ta shiga taja hannun shi ta zaunar da shi kan bed ta share mai hawaye tace "haba Hakeem me yake faruwa da har ka kasa nuna jarumtar ka akai waye ba lafiya a cikin ku" umma meyasa pinky zata min haka yanzu gashi tana so taja mana matsala.....me tayi kuma wace irin matsala take qoqarin ja mana ? Pills take sha ba izini na kuma ashe pills d'in matsala ne da shi lalata womb yake kai tsaye......subhanalillahi ita kuwa wannan danyen aikin fa wacce bata ga ta kai ga  d'a ko qwaya d'aya ba har ta fara planning,lallai bata kyauta ba ko kadan amma kayi haquri kasan Billy ba wasu shekaru ne da ita ba har yanzu ko ashirin bata cika ba,sannan me ya jawo kuka je asibiti?ciwon mara ta fara dashi sannan ta shiga yin bleeding  sosai shine koda muka je asibiti Amjad yace pills ne tasha yasa take bleeding.
yanzu fatana umma kar ace yayi ma mahaifar ta  illah shiyasa na shiga rud'ani ganin kallo daya Amjad yayi wa pills din naga duk yabi ya rikice yana gaya min illar sa yayinda na hango damuwa qarara a fuskar sa, gashi kinsan Amjad mutum ne wanda baya nuna damuwar sa kai tsaye sae dai idan damuwar ce tafi qarfin sa ,
 kinga kuwa umma dole na shiga damuwa domin ko kadan bana son pinky ta shiga matsala komai qanqantar ta kuwa amma na fahimci sam pinky bata fahimci yanda nake jin ta a raina bane shiyasa take abin da taga dama har tana min wasa da rayuwar ta,,,
ya isa haka ai kuka bai dace da namijin mutum irin ka ba,
sae kace ba soja ba, umma ba soja ba koma mene ne ni indai akan pinky ne bazan iya 6oye damuwa ta ba  sbd samun matsalar pinky tamkar rugujewar rayuwata ne gabad'aya shiyasa bazan iya controlling kaina ba.... take heart Hakeem u have to calm down kaji yanzu ka tashi muje a maida Billy asibiti muji idan ba wata matsala ko hankalin mu zai kwanta,
nan ta rarrashe shi suka fito,
inda da qyar Billy ta samu ta tashi tazo gurin Hakeem,
qoqarin kauce mata yake tayi saurin riqo hannun shi ya fizge hannun shi da qarfi gashi Billy ba wani qarfi take ji ba qarfin hali ne kawai take har tana tafiya ,
ai kuwa ta tafi suuuu zata fadi, Hakeem ya kamata da hanzarin sa  yana kallon yanda ta runtse idanun ta gam ta kuma dafe qasan cikin ta, durqusawa tayi gurin shima yayi saurin durqusawa yana kallon ta yace "pinky kinji ciwo ne? komai kasa ce mai tayi domin ko magana bata iya yi,
nan ya shafo gefen fuskar ta cike da damuwa ganin yanda take zufa yace"  umma please ruwa, nan umma ta kawo mishi ruwa ya jinginata a qirjin sa ya bata tasha ya zaro handkerchief ya share mata zufa sannan ya tallabe ta cak yaje ya kwantar kan seater har yanzu idanun ta a rufe suke yayinda Hakeem ke durqushe kan guiwoyin sa yana qara share mata zufa kan goshin ta ,
 pinky ta jimqe hannun sa gam kamar wacce zata fasa mishi hannu ta riqo d'ayan hannun sa ta d'ora kan qasan cikin ta tace " Bobby ka taimaka ka cire min zan mutu nan ta shiga kuka sosai tana roqon ya cire mata kar ta mutu,
kuka Hakeem ya kama mata yana nuna ma umma jinin da ke fita qasan Billy yana gangorowa jikin seater, yace" kinga yanda take bleeding ko umma!
umma ta shiga salati tace" ni kuwa Billy wai wane irin pills ne kika sha haka? ban san pills nake sha ba umma bani shi akayi a matsayin wani magani...... waya baki maganin? Mama ta bani shi lokacin da muka je nuna musu mota ...... Hajiya seema? Eh umma may be ita ma batasan pills bane shiyasa ta bani.
nan umma ta nemi ganin maganin Hakeem ya bata tace"is not about may be she no everything tana sane da cewa pills ne ta baki sbd wani qudiri nata kan abinda kika mata take son d'aukar fansa.
  Hakeem! yi maza kayi mata wanka kuje asibiti ni zanje na sami Hajiya seema.....no umma kar kije ba tare da tabbacin cewa da sanin ta ta bata pills d'in ba.... Ni ko nake da tabbaci hakan Hakeem don haka kayi ka shirya ta kuje asibiti kawai in yaso daga can zan same ku asibiti,
tana gama fad'a ta fita  Billy sae kallon Hakeem take dake dauke da hawaye a fuskar shi kamar mace,
a hankali ta shiga share mishi hawayen yayinda yake share mata nawa hawayen cike da tausayi.
Nan ya dauke ta cak suka haura sama yayi mata wanka ya shirya ta suka kama hanyar asibiti.


*Billy giro 😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/6, 11:19 PM] ‪+227 89 92 39 69‬: 💃🏻💃🏻MAKIRA..... 💃🏻💃🏻

©FIRDAUSI SODANGI 💅🏻
              &
FERTYMERH XARAH 💞

       115 to 120

    Da kyar ya bari Aka gama meeting din Ya nufi gida,

Yana shigowa da sallama ya soma cin Karo da maryam da Ahmad xaune a falon,

Suka amsa masa suna kallonsa da mamaki rabonsa da sallama tun kafin yayi aure🙄

Ahmad baiyi mamaki ba cos yasan abinda a nan,

Ina ummanku,ina Fatymah da Hasheem?

Maryam Tace su umma na ciki Abba, da Sauri Ya nufi dakin

Umma tayi mamakin ganinsa dakinta Fatymah na gefenta tana tausa mata qafafunta,

Abba sannu da xuwa, da murmushi Ya amsa
'sannu auta, Ya juya yana kallon umma itama shi take kallo Fatymah ta fita da Sauri Ya qaraso kusa da ita ya xauna,

Hajiya kina fushi dani kina min kallon mamaki ne Wlhy bnsan meke damuna ba kullum kuna raina haka yau Naji ni wani iri kamar ba niba, Dan Allah Ki yafemin,

Baka min komai ba amma Inaso ka Yawaita addu'a da karatun Qur'an Idan ba haka ba baxaka daina jin Wannan nauyin dake kanka ba,

Nagode, yau me aka tanadar min ne, ina jin yunwa,
Me kakeso daga gareni?
Komai ma Inaso, ki hadamin bara na duba Firdausi na dawo, ta bisa da kallo hr ya fice,

A dakin Fyn gal tana ganinsa Ta soma matse hawaye,

Dear sun hanamin abinci ina jin yunwa yaron cikina sai juyawa yake,

Subhanallah kuma sai kika xauna da yunwa, miya hana Ki girka kici tunda akwai komai a store, bani key din store din.....

Shiru tayi Tana kallonsa da mamaki

Mike faruwa Mike damun Alhaji miyake nufi Ya daina tsorontane kome? Kardai mgn boka Ya daina aikine, aikinsa baya da nasaba da Wannan tukunyar da Ahmad ya gani.,

Kinyi shiru ina mgn me kike tunani, muryarsa ta katseta
Tace ba komai taje ta dauko tabashi jikinsa na rawa, ya juya yana fadin ki xo,

Yana tafe Tana bayansa hr store, Duk suna falo suna kallonsu,

Ya bude store din ba komai aciki duk an kwashe, ya juyo yana kallonta

Duk ina kayan dake Wannan store din?

Jikinta na soma rawa tana inda inda
Nima bnsaniba,
Kamar Ya baki sani ba inaji key din na hannuki ko
'oh na manta umma batada abinci sai na bada akai mata sauran na rabawa danginka

"kin raba masu shine ba wanda Ya kirani ya min Godiya, bn yardaba xn bincika, girki kuma ba wanda xai sake maki kici, Kema xaki riqa girki a gidannan kuma tare da yarana kin fahimceni? Ta gyada Kai tana kallonsa idanunta taf da hawaye

Ya juya Ya xauna kan dinning table umma ta soma hada masa abinci, Ahmad da maryam suka bar falon sashensa ya nufa da ita,

Ta kwanto ta bayansa tana murmushi
Yaya Ahmad I feel so happy today umma da Abba sun shirya, ya xagayo da ita ta gabansa,

ai dama ba fada sukayi ba aikine kawai irin na malamai, ya gaya mata komai,

Tayi far da ido tana kallonsa kafin ta tashi, ya janyota ta fado jikinsa

"ina kuma xakije,
Ta janyo hannunsa ta Dora akan cikinta
"yaya Ahmad ina jin yunwa pls ka Barni,
'Nima ina jin yunwa feed me first, kafin tayi mgn ta sanya bakinsa a nata, suka fada duniyar ma'aurata

(Qawata Fido ta kalleni, pherty muje Kar mu sanya masu ido, na tunxure baki na bita badan naso ba amma da sai naga komai😀😉)

*

Kwana biyu ba canji Duk da ta Kira mamanta ta gayamata kuma ta Je gurin boka Ta karbo mata magani hr a abinci ta sanya masa amma ba wani canji,

Ta shirya da kanta taje gurin boka

Keeeee! Ya daka mata tsawa,
Buqatarki baxata biya ba hr sai na qara kusantarki kamar farko😳🙊,Idan ya kusance Ki xaku dawo kamar farko,

Na amince boka(wa'iyaxubillah, Allah ka qara tsare mu ka kuma tsarkake xukatanmu, 👏🏻)

Yayi wata irin dariyar da sai da dajin ya dauka,
'Ki shiga daga ciki kiyi xir kafin na shigo,

*****

A wahalce ta shigo gidan yau ba sauqi ynda boka yayi mata kaca kaca da kyar ta iya gasa kanta da ruwan xafi,

Ta Kira maman take gayamata komai daidai lokacin Abba Ke shigowa
"Tor umma Ya xanyi dole xn amince masa saboda Kinsan cikin nan ba nashi bane......tayi shiru sakamakon hada ido da tayi da Abba a bakin qofar dakin.

Fido💅🏻
Pherty🎤👯
[9/22, 8:31 PM] ‪+234 810 038 8117‬: , [07/9/2016]

*👛BILLY PINKY DURLING 👛*



*Billy giro 😊*


*Page*
     *👛 71&72👛*
A 6angaren umma kuwa tana shiga gidan Abban Billy take d'an jin wasu suruttai a cikin falo hakan yasa ta d'an dakata bata qarasa shiga ba sbd yanda take jin sunan Billy na fitowa a zancen su kan pills d'in sa suka bata sae murna suke domin Hajiya seema ta gansu a lokacin da su Hakeem suka kai Billy asibiti yayinda taje dubiya.
   Ran umma ne ya qara 6aci da kuma mamakin mugun nufin su na gaba akan Billy.
Da hanzarin ta zata shiga falo domin ci musu mutunci Abban Billy ya dakatar da ita wanda tun dazu yake gefen ta bata sani ba kuma duk yaji abinda Hajiya seema ke fad'i ita da qawar ta.
 A tare suka shiga falon shida umma suka same su sae ci gaba da kekkewa suke suna tafawa qawar Hajiya seema ce ta fara hango su tayi saurin yiwa Hajiya seema nuni da ido a rikice Hajiya seema ta miqe tsaye tana kallon su ba wata wata Abban Billy ya kife ta da mari tare da furta kalmar saki a kanta, umma tace "subhananlillahi ya zaka furta kalmar saki kai tsaye a cikin fushi..... Saki ya zama dole a tsakani na da ita domin duk matar da ke qoqarin ganin ruguza rayuwar 'yata ba matar zama bace kuma bata dubi irin adalcin da na mata ba naqi qaro aure bayan nasan ta sami matsalar da baza ta sake haifuwa ba duk da ina cike da son 'ya' ya amma na haqura shine bata ga abinda zata saka min da shi ba sae lalata min rayuwar 'yata kwaya d'aya tal sbd kawai ta zamo ita ce silar samun matsalar ta.... cikin kuka Hajiya seema ta durqusa kan guiwoyin ta tace "don
 Alhj kayi haquri wlh sharrin shaid'an ne..... hannun sa yasa ya buge hannun ta da riqe mishi babbar riga ya juya zasu bar gidan shida umma tayi saurin cin gaban su tana roqon umma kan ta roqa mata shi ta san yana  jin maganar ta.... wani mugun kallo umma ta sakar mata tace "azzaluma kawai macuciya! taya kike tunanin kinyi matsayin da zan roqa miki alfarma! bayan kina neman illata rayuwar er mu! sae dai ma nace Allah ya isa tsakanin mu da ke..... na shiga uku don Allah Halima (cewa da qawar ta) kiyi musu bayani wlh ko d'aya bana da nufin cutar da Billy kece kika bani shawar yin hakan...... Da Allah malama ni sake ni don na baki shawara sae akace dole sae kin bi! soro soro Hajiya seema tayi tana kallon Halima inda ta tuna lokacin da take kwance kan gadon asibiti Halima ta same ta tana mata ya jiki hade da jajanta mata har tana cewa wai garin ya hakan ta faru? wlh qaddara ce Halima Billy ce ke ball ni kuma ina zaune ina shan iska tashin da zanyi kawai naji qwallo a cikin qafafu na hakan yasa na fadi kan tsofon ciki na, nan na buga ihun da tun daga lokacin bansan inda kaina yake ba shine koda na farfad'o na ganni a asibiti bana tare da tsofon ciki na koda na tambayi Abban Billy  ina abin da na haifa,
ya shiga gaya min sae dai nayi haquri abinda ke cikin cikina d'a namiji ne kuma ya fito ba rai sanadiyar far masa da nayi..... innalillahi wa Inna ilaihi raji'un! seema yanzu duk irin wahalar da kika sha kan laulayin cikin nan ace abinda ke ciki ya fito ba rai.... Halima da ace shi kad'ai ne da da sauqi yanzu fa shike nan  bazan qara haifuwa ba sbd likitawa sunce mahaifata ta sami matsala..... What! keda haifuwa har abada kuma har kike kiran abin da qaddara.... me zan Kira abun idan ba qaddara ba Halima? Hmm! Lallai ke kidahuma ce mara tunani to ai da gayya aka miki haka domin na tabbatar baqar matar nan ce umman Hakeem ta turo Billy ta miki haka don kawai ki sami matsala da ke har abinda ke cikin cikin ki sbd kar ki sami qaruwa kizo nan gaba ki fita da y'a'ya ganin Hakeem ne kad'ai d'anta kuma har yanzu shiru ba alamun zata sake haifo wani don haka kar ma ki yadda da hakan ba qaddara bace.... Hm Halima ai kin fi kowa sanin nida umman Hakeem ba ma wannan kishin da matan sauri keyi ni mutunci ne tsakanin mu don haka ki ajiye wannan zancen kawai..... Kin yarda da qaddara ce kenan kuma a haka zaki zauna har abada ba ke ba haifuwa sae dai ki gani a gun wasu matan se kace kin rako mata duniya.... Halima don Allah ki ajiye wannan zancen  bana so,
na yarda da qaddara kuma zanci gaba da haquri kan yanda Allah ya tsaro min rayuwata.

  Duk wannan tunanin yana faruwa ne yayinda take gaya musu komai cikin kuka sannan taci gaba da cewa haka tayi ta bani muguwar shawara har nazo na fara jin haushin Billy da umman Hakeem shine kuma yanzu ta bani shawara kan cewa na lalata mahaifar Billy  amma shine Halima baki ga abinda zaki saka min dashi ba sae haka bayan kece kika bani shawara....... Mtsw har wa yau ke kidahuma ce kuma marar tunani in banda rashin tunani baki san shawara mai kyau da mara kyau ba ko kuwa idan nace ki fad'a wuta zaki fad'a wuta ne to bari kiji in gaya miki abinda baki sani ba, ba Billy ce ta jefo qwallor ba nice sbd na jima ina baqin cikin ganin ci gaban rayuwar ki kinyi aure kin barni har yanzu banyi auren ba sae faman yawo nake kan titi  shiyasa na shiga baki baqaqen shawarwari  don kawai naga cewa naki auren ya mutu inda sae yau Allah ya cika min burina sae dai nace miki sannu da abinda ya faru da ke, ni kinga tafiya ta,
nan ta d'auki jakar ta tana mata kallon wulaqanci ta fita.
wani irin kukan nadama ne yazo mata taji komai ya cakud'e mata.
  Nan su umma suka barta suka wuce zuwa asibiti.


Sae zuwa dare suka dawo ko shi Billy ce ta matsa bata son kwana asibiti amma ba'ayi niyyar sallamar ta ba.
 
Hakeem ne ke mata shirin bacci bayan ya gama ya had'a mata tea mai kauri ya bata tasha sannan ya bata magunguna tasha yasa tissue ya share mata bakin ta ya kwantar da ita kan qirjin sa yana mata sannu yayinda yake shafar bayan ta a hankali, qara shigewa tayi a qirjin sa tana share hawaye cike da son kar ya ganta, Hakeem da duk wani motsi nata yana kule dashi yace "Billyta me kike ma kuka ko har yanzu sosai marar ki ke ciwo? girgiza mai kai tayi yayinda ya shafo qasan cikin ta a hankali yace to mene ne? akan Abba ne da mama banji dadin yanda ta biye wa shawarar qawar ta ba har tazo ta kai ta ga haka n.... Billyta ki ajiye wannan zancen domin haushi yake bani na rasa me yake damun wasu mata da suke biye wa shawarar qawaye daga qarshe suzo suna yin nadama .
  Ni yanzu ba abinda yake damu na irin na samu ki daina bleeding  ko zamu qara samun tabbacin lafiyar ki duk da cewa bincike ya nuna mahaifar ki lafiya lau take bata da wata matsala.

Har kusan two weeks pinky na faman bleeding hakan yasa ko yaushe suna kan yawon asibiti duk Hakeem ya rame sbd yanda ya shiga damuwa haka ita ma Billy duk tabi ta rame kan zirzirga da yawan shan allurai wanda duk za'ayi allura sae tayi ta faman kuka.

Zaune take gaban madubi d'aure da towel tana shafa turarukka duk d'akin ya qamsashe .

Tana gama shafe shafen ta ta tashi sae ga Hakeem ya shigo d'akin sanye da uniform din sa na sojawa ya lumshe idon shi tare da sauke ajiyar zuciya sbd jin dad'in yanayin d'akin luf luf ga sanyin Ac da qamshi.
Billy wacce ta zaro rigar da zata saka ta saki rigar ta tafi cikin murna ta tarbi Hakeem haka shima Hakeem da murnar shi ya tallebeta yaje kan bed ya zauna tare da zaunar da ita kan cinyar shi yace "Billyta ya ake ciki ne naga sae murna kike ko kin daina bleeding ne ? gyada mishi kai tayi yayinda take wasa da buttons d'in rigar shi,
fuskar ta na d'auke da murmushi,
yace" Alhmdlh ina ce komai normal kike ji a jikin ki ba wata matsala ko ?ta lumshe idon tare da fad'in "eh"
zuruf taji hannun sa cikin towel yana lalubar qirjin ta yana matsa su a hankali yace"abokanan wasa ta fa na jima ban tambayi lafiyar su..... kunya taji tasa tafukan hannyen ta ta rufe fuskar ta,
Hakeem yayi murmushi yana kallon ta sbd sosai yake son ganin yanayin pinky idan taji kunya hakan yasa wani lokaci da gangan yake mata wani abun don kawai yaga yanayin jin kunyar ta.
   Jaye hannyen ta yayi yaje a hankali kan lips d'in ta ya bata kiss yace "pinky wai har yanzu kunya ta kike ji" murmushi kawai ta mishi tare da kwantar da kanta a kafad'ar shi sae yawo take da yatsan ta kan qirjin sa kamar mai zana wani abu yace "muje ki taya ni wanka na samu nazo naci abinci nan ta taya shi ya cire kayan jikin sa ta d'auko towel ta d'aura mishi suka je toilet.

Sun jima a toilet d'in inda naga pinky ta fito  cike da dariya har tana had'awa da d'an gudu gudu haka Hakeem ya biyo bayan ta, ta fa'da ruf da ciki kan bed shi kuma Hakeem ya juyo da ita ya fad'a kan jikin ta ya mata rumfa, pinky cikin dariya take cewa "nidai Bobby kaje ka d'aura towel tukun..... bazan saka ba sae na rama abinda kika min nan ya zare mata towel sae abubuwa yake kan jikin ta tana faman dariya tana zizzille mishi tana fad'in ya isa haka Bobby ai bada yawa na maka ba ganin bazai daina ba ita ma ta mirgina ta dawo ita ce saman shi tayi mishi rumfa sae abubuwa take mishi haka sukayi tayi wannan ya koma saman wannan, wannan ya koma saman wannan sae da suka gaji sukayi kwance rairan suna dibin silin sae sauke numfashi suke suna dariya Hakeem ne ya mirgino kan jikin pinky yayinda qirjin su ya had'e guri d'aya sae kallon juna suke idanun su duk sun soma canza kala kan sha'awar da suka tayar wa junan su garin wasa.
  A hankali Hakeem yakai bakin sa kan na pinky ya zira harshen sa a ciki yana tsurar lips d'in ta cikin natsuwa kamar wanda ya sami hadadden sweet d'in da baya so ya qare mishi, cikin haka ne  ya kai hannu yana wasa da qirjin ta.


*Billy giro 😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 8:34 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [08/9/2016]

*👛BILLY PINKY DURLING 👛*






*Na Billy giro 😊*



*page*
    *👛73&74👛*
Da haka ne pinky ta shiga mayar mishi da martani suka dauki lokaci suna abu d'aya suna cikin haka ne wayar Hakeem ta shiga ruri ba wanda yaji a cikin su duk hankalin su ya gushe can Billy taji ta samu da qyar ta dakatar da Hakeem ta d'auko wayar ta bashi bai iya kar6ar wayar ba sae  rungume ta yayi yana sauke numfashi tare da sai saita kan shi sannan ya kar6i wayar yaga har 10 missed calls.
    Nan ya kira bai wani jima ba ya gama wayar tare da zare jikin sa cike da damuwa, sae kuma yayi saurin 6oye damuwar shi sbd ganin Billy a side din sa, rungume ta yayi yana shafar jikin ta cike da buqatuwar kasancewa da ita,
can ya daina shafar ta, ya dafe goshin sa yayi shiru, Billy ta kalle shi da kulawa tace "my soldier man mene ne?sauke numfashi yayi yace" Billyta tafiya ce ta kama ni yanzun nan wai za muje bauci gun wani meeting kuma zamu yi two days"
tausayin shi taji sbd ta fahimci cike yake da son kasancewa da ita hakan yasa ta kwantar da kan shi a qirjin ta tana shafa sumar kanshi a hankali har sae da taga ya d'an sami natsuwa tace "to muje kaci abinci kaji,
nan ya yaye bedsheets din jikin shi ya jawo towel  ya daura ita kuma taja bedsheets taje ta dauki rigar ta ta saka sannan ta fita,
koda ta dawo har ya saka wando da singlet yayi zaune kan bed dafe da goshi,
stool taja ta kai kusa da shi tare da d'ora plate d'in abincin akai,
ta kai hannu tana ta6a goshin sa tace
"Bobby lafiya? ba komai, hakan tayi shiru ta fara bashi abinci,
ci yake amma ta fahimci kwata kwata baya jin dad'in abincin sbd buqatuwar da yake ciki haka tayi ta lalla6a shi har ta samu ya cika cikin shi ta bashi lemu yasha sannan ta kai babban yatsan ta ta share mishi lips kafin take zaro tissue ta qara goge mishi,
 riga ta saka mishi
     sannan ta nemo takalma ta saka mishi.
  Turare take fesa mishi
     yayinda take kallon  yanayin shi komai jiki a sanyaye yake yin shi,
    sae duk taji ba dad'i tace "uhm uhm Bobby zan yi kuka fa" yayi saurin kallon ta tare da shafo gefen fuskar ta yace" meyasa Billyta?turo baki tayi hade da d'an bubbuga qafafun ta a qasa alamar shagwa6a tace "to ai kaine kaqi sakin jikin ka , ina sama turare kayi tsaye ko d'an rise in hannayen ka baka kayi ba, yayi murmushi tare da kama kunnen shi yace" sorry"
ita ma murmushin tayi ta dauko jakar shi ta kalle shi tare da "fadin baka ji ba" ya karkad'a kunnen shi hade da d'an russunar da kanshi yace" yauwa tawan fad'i ina jinki" ziruf yaji harshen ta cikin kunnen shi tayi mishi wani abu mai cike da sa dariya ta fito da gudu ya biyo ta suka fito gurin motar shi sae dariya suke nan ta miqa mishi jakar shi bai kar6a ba sae da ya mata peck kan kumatu inda ya shiga mota cike da nishad'i suna yiwa juna bye bye
 sae da taga fitar shi ta koma daga ciki ta fada ruf da ciki kan seater tana kuka sbd tunanin two days din da za tayi ba tare da Hakeem ba wanda tun lokacin da ya gaya mata zancen tafiyar take jin kuka amma ganin ya fi ta shiga damuwa yasa ta 6oye ta ta damuwar kar abubuwa su mishi yawa.

Yinin ranar a 6angaren umma ta yini har ma ta kwana a can.

Guraren 11am  pinky ce a kitchen nan 6angaren su umma tana had'a cake.
rungume ta taji anyi ta baya, ta juyo tare da sake ihun murna ganin Hakeem ne,tace "Bobby shine baka gaya min zaka dawo ba" Billyta ni kai na ban san zan dawo ba, na zaci zan iya jure two days amma na kasa, ya fad'i haka ne tare jan hannun ta yace "zo muje... Bobby ai ki nake yiwa umma fa zata yi baqi ne.... kamar wanda zai yi mata kuka yace" to Billyta kinsan abinda nakeji kuwa ko so kike na mutu.....
Bobby....
nifa bazan saurari me zaki ce ba kawai muje.
  Nan yaja hannun ta suka fito Billy na ganin Baraka tace "yauwa Baraka don Allah jeki qarasawa umma aikin da na bari" tace "to " kafin suke fita.

Suna shiga 6angaren su Hakeem ya zarce da ita d'akin shi bai tsaya wata ba ya raba su da kayan jikin su suka fad'a kan bed sauri sauri yake aikamata saqonni yana shan mammanta tamkar mayuwanci jinjirin da ya jima bai sha mamma ba, haka yake abubuwan sa a gaggauce har suka fad'a duniyar ma'aurata wata irin ni'ima Hakeem ya tsinci kansa a ciki inda har kuka sae da yayi ma pinky  ya kuma nemi yayi second round,
pinky bata hana shi ba sbd mugun tausayi ya bata amma ta wahala sosai kafin yake barin ta sae zogi take ji sbd yanda tasha wahala.

Tunda Hakeem ya samu gamsuwa yake kwance a qirjin pinky daga nan bacci mai nauyi ya d'auke shi sae da baccin shi yayi nisa ta shiga gyara mishi kwanciya sae lalla6a shi take kar ya farka kamar wani qaramin yaro.
  Knocking taji ta zare jikin ta a hankali ta nemi towel ta d'aura ta bud'e qofa umma ta gani hakan yasa taji kunya sosai,
tayi saurin duqar da kanta bcs ta d'auka feenah ce sbd ita tace mata zata zo, umma tace "lafiyar ki kika dawo kika tu6e kika bar min aiki a hannun Baraka?
yi haquri umma.... qarar bude qofa suka ji koda Billy ta juya Hakeem ne ba shiri ta maida shi ciki ta rufe qofar sbd haka ya taso abin shi ba komai a jikin shi duk taji kunya sae kame kame take, duk da umma bata ga tsiraicin sa ba amma ta fahimci ba kaya yake qoqarin fitowa,murmushi tayi had'e da girgiza kanta tace "Allah ya shirya min kai Hakeem, shifa haka ya taso tun yana yaro bashi da kunya uwa uba yaje qasar turawa yayi karatu, tukuna ma yaushe ne ya dawo? ina kan aiki ya dawo, to shike nan kima yi zaman ki har ku qarasa abinda kuke bcs an kammala komai, da kunya tace "umma ai ba wani abu muke yi ba bari kawai nazo" umma tayi murmushi tace"na ce miki an kammala komai ai "
nan ta tura Billy cikin d'aki ta jawo qofa ta rufe ta bar 6angaren cike da murmushi.


Billy kuwa umma na tura ta cikin d'aki ta kalli Hakeem cikin fishin shagwa6a yayi saurin kama kunnen shi yace" yi haquri Billyta Allah ban san da umma a gurin ba"
ya fad'i hakane yayinda ya taso yaja hannun ta ya rarrashi abar shi suka shige blanket sae bacci.

Sun jima suna bacci koda Billy ta farka bata ga Hakeem ba,
toilet ta fad'a tayi wanka tana fitowa ta sami Hakeem zaune kan bed sanye da farar singlet da farin three quarter ya d'ora laptop kan stool yana wani aiki.
  Kan  bayan shi taxo ta kwanta yayinda gefen fuskar su ya had'u guri d'aya tana kallon aikin da yake,
ya shafo gefen fuskar ta yace "Billyta kin tashi? eemm, yauwa je kiyi sallah kizo muci abinci umma ta aiko da shi kinji, ba musu ta tashi ta shirya tayi sallah suka ci abinci.
  Bayan sun gama ya d'auki laptop din shi yace" Billyta zan je falo bcs ana so na hallar ci meeting din da za'ayi ta video call"nan ta gyad'a mishi kai tare da fadin" please Bobby ni kuma ina so naje 6angaren su umma ashe Feenah taxo tun d'azun shine umma tace ta jira ni a can sae yanzu naga text d'in ta, ok to muje.
  Nan yaja hannun ta suka fita tare ya tsaya a falo ta wuce 6angaren su umma.


Bayan wata d'aya da sati biyu tuni Billy ta koma school har ma sun fara exams kasancewar ko da ta koma semester tayi nisa.

Naini, Feenah, Bobby sune zaune a kan dining suna cin abinci, Feenah tace "ihm wai ni Hakeem yaushe ne pinky zata fito bayan tasan tana da manyan manyan baqi Naini yayi tafiya ya dawo amma ko ta fito su gaisa ko kuma yau sae an yanka ticket muke samun ganin ta?
 um um ba haka bane..... to ya ne tun d'azun fa naga kayi mata knocking amma taqi ta fito gashi har mun gaji da jiran ta mun fara cin abinci,  haka ne dama nayi tunanin baza  ta fito ba.....au sarautar ce ta motsa oh i got it Bilqisu mai gadon zinari ai dole tayi sarauta.....uhm Feenah kenan ba haka bane Billyna fushi take yi dani kan  nayi mata fad'a na kuma sa aka mata allura sbd rashin lafiyar da take fama da ita kwana biyu, gashi kuna exams ina gudun kar ciwon yazo ya mata yawa shine fa na tirsasa aka mata allura inda ta shiga yin fishi dani tun safe har yanzu.... Uhm lallai pinky najin dad'in ta da yawa, Hakeem yace "bani wayar ki na kira ta nasan zata d'aga,
nan ta bashi wayar ya kira yace"Billyta kiyi haquri ki fito kinji su Naini da Feenah tun d'azun sun zo suna jiran fitowar ki" bata ce mishi komai ba ta katse wayar ya bawa Feenah waya ba jimawa sae gata ta fito.
nan ta saki fuska kamar ba wani abu ta gaisa dasu sukayi mata ya jiki sannan ta sami guri ta zauna Hakeem ne ya zuba mata farfesun kifi da kanshi sbd shine favourite d'in ta.
ba musu tabi sahun su tana cin abinci sbd yunwa take ji sosai Hakeem sae kallon ta yake sbd tun da ta fito bata kalli ko gefen da yake zaune ba yana cikin kallon ta ne yaga tayi saurin ture plate tare da saurin rufe bakin ta sbd yunqurin aman da ya zo mata,
nan ta tashi ta tafi da gudu tana son haurawa sama bata sami hauwa ba amai ya kufce mata wanda yayi dai dai da isowar Hakeem yayi hanzarin cire rigar jikin sa ya shimfid'a tana ci gaba da kwara amai akai,
ba qaramin galabaita tayi ba domin aman har ta hancin ta yake fitowa da qyar ta samu ya tsaya sae numfashi take sama sama Hakeem da ke durqushe kusa da ita ya jawota jikin sa yana mata sannu sae kuka take dafe da cikin ta da ke mata mugun ciwo, feenah ce ta kawo ruwa a cup da rubber bowl,
  Hakeem ya kar6i ruwan ya bata ta kurkure bakinta ta zuba a bowl, nan feenah ta kira Baraka ta d'auke kayan aman ta goge gurin tsaf da  turaren mopping mai dad'in qamshi,shi kuma Hakeem ya zaro handkerchief ya d'an jiqa shi da ruwa yana share mata fuskar ta ita kuma sae faman kuka take tana qara narkewa kan jikin shi.
     Ba shiri ta sauka kan jikin shi ta shiga kwara wani amai sbd qamshin turaren mopping da ya daki hancin ta.

*Billy giro 😊*
👛👛👛👛👛👛👛[9/22, 8:37 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [13/9/2016 ]

*👛BILLY PINKY DURLING 👛*



*Na Billy giro 😊*


*Page*
      *👛79&80👛*
Ya jima kafin yake fitowa ya samu har lokacin Billy kuka take,
yayi tsaye yana kallon ta.

Cikin fushi ta tashi ta fita ya bita da ido yayinda ya qara jin kansa da 6acin rai har yana jin kamar ya bita yayi ta yi mata fad'a,
sae dai kuma da ya tuna cewa tunanin shi da nata ba d'aya bane kuma shine babba shine ya kamata ya sauko yaje ya rarrashe ta.
 Nan ya bita falo  ya samu ta had'e kai da guiwa tana faman ci gaba da kuka,
ya zauna kusa da ita tare da dafa ta tayi saurin jaye mishi hannu, inda ya shiga magana cikin muryar lallashi yace " Billyta ki daina kukan nan haka ba kya gudun ciwon kai ne,
gashi kuma kinsan ba kya da isassar lafiya"
ya fadi haka ne yayinda ya jawota jikin sa zai share mata hawaye,
taso ta fizge jikin ta daga nashi sbd ya 6ata mata rai kan tsawar da ya daka mata,
sae kuma taga in tayi hakan ba riba gara ta haqura ta kuma lalla6a shi ko zai yarda da abin da take so.
Nan ta qara lafewa  a jikin shi ta d'ago da idanun ta da suka cike tap da qwallah tace" please Bobby ka taya ni yaqin nan ko Abba zai amince ya maida mama tunda tayi nadamar abin da ta aikata kuma tun lokacin cikin aiko masa saqon ban haquri take,
kauda kansa yayi domin ko kad'an baya son tana mishi maganar mama kan illata Billy da taso tayi sae duk yaji ya tsane ta har baya son yaji an ambace sunan ta, Billy ta juyo da fuskar sa wacce ke d'auke da damuwa tace " please Bobby dan Allah dai"
  Kallon ta yayi yayinda zuciyar shi ke ta ingiza shi kan ya daka mata tsawar da ko da kuskure baza ta qara tuntu6ar sa da wannan zancen ba, amma ganin yanda take ta lalla6a shi yasa ya danne duk wani abu da yake ji ya shiga share mata hawayen  da suka gangaro sannan yace" naji Billyta zan yiwa Abba magana "
sosai taji dad'i har tana mishi godiya nan yaja hannun ta suka haura sama domin sanya tufafi kasancewar kowanen su towel ne dashi.



After 1 week

8:30pm

Hakeem ne tsaye a jikin mirror ya fito daga wanka yana goge sumar kanshi da d'an qaramin towel.
 Billy ta shigo d'akin sanye da er fincikar rigar bacci handless iya cinye yayinda ake hango rabin mamanta a waje sbd yanayin style d'in wuyan rigar.

A hankali ta rungumo Hakeem ta baya inda suke hango juna ta jikin mirror, murmushi suka sakar wa junan su,sannan ya zagayo da ita ya xaunar da ita kan cinyar shi, ya kai d'an yatsan shi kan tsagin mammanta yana yawo da shi,
cikin hikima Billy ta jaye hannun shi sbd tasan in ya fara wasa da abokan wasan shi ba daina wa zai yi ba.
    Kiss ya dorawa qirjin kafin
Billy ke cewa"godiya nake my soldier man naji dad'in yanda Abba ya haqura ya maida mama but pls gobe zaka bar ni naje gidan?

Shiru ya mata yayinda murmushin fuskar shi ya 6ace,
ya Kalle ta sau d'aya ya kauda kai,
nan wayar shi tayi qara yace " d'auko min waya ta " wanda kafin yace hakan tayi niyar d'auko mishi wayar sbd tana tunanin Abban ta ne ya kira bcs tana cikin waya da shi ne cajin wayar ta ya qare sea tayo d'akin Hakeem.
    Da hanzari ta tafi d'auko wayar tana fad'in "yeah Allah yasa Abbana ne" .......qara ta saki sbd fad'uwar da tayi kan wani jiri da ya d'ebe ta.
   Ba shiri Hakeem ya jefar da d'an qaramin towel d'in da ke hannun shi yana isa ya tayar da ita ta fada kan qirjin sa da qarfi duk tabi ta qanqame shi tana kuka kamar wacce ta tsorata
hakan yasa Hakeem ya d'ago fuskar ta tare da fad"in "Billyta mene ne, me ya kayar da ke?tace" wani irin jiri ne ya d'ebe ni har naga d'akin yana juya min kamar zai fad'o min" oh no sorry but a u ok?  "am ok" nan ya kwantar da kanta a qirjin shi yana mata sannu shafo cikin ta yaji tayi yayi saurin kallon ta tare da shafo cikin yace " wani abu ya sami babyn mu ne? girgiza kanta tayi tace" um um ba komai.....no tashi muje asibiti a duba bcs hankali na yafi kwanciya da hakan nan suka shirya sae asibiti bayan an gama duba ta Amjad yace "fad'uwar da tayi bai illata babyn ba amma ta rage dogon motsi sosai sbd hakan kesa taji jiri ya d'ebe ta kai tsaye kuma dama ba a cika son mai ciki na fizgar jikin ta ba, har dai ga mai sabon ciki then ga wasu magunguna da zan rubuta ma sea ka siya mata su ta riqa sha nan Hakeem ya kar6i takarda tare da sauke ajiyar zuciya yayi ma Amjad godiya kafin yake riqo hannun Billy yace "muje"

Har suna batun fita Hakeem ya juyo ya kalli Amjad da ba'a yace " doctor ko har da tafiya kar na sake bari tayi na riqa d'aukar ta..... Amjad yayi dariya yace" Baban soyayya to ko haka ne ai baza ka iya ba.... wa ya gaya ma Billyta ce fa,i know amma zai maka wahala..... to wane aikin wahala ne banyi ba nida nayi soja..... hehe ai ba zancen soja bane maza ne basu da tabbas sae kun fara d'and'anawa mutum dad'i kai tsaye ku daina koda hakan baya wahal da ku kuwa, Hakeem ya kalli matar Amjad wacce shigowar ta kenan tayi magana.

yace " wasu mazan dai don ni bana d'aya daga cikin su ko Billyta? hm Bobby kenan  a bar zancen kawai....gara da kika ce haka domin yanzu baza ki gane halin d'a namiji ba sae rayuwa taci gaba inda ke zakiyi ta haquri kina danne zuciyar ki ki samu ku zauna lafiya tare da fatar kar hawan jini ya kama ki.......a'a fa kar ki tsora ta min Billyta,wlh Allah ina sonta bazan so na nuna mata halin d'a namiji ba.....dariya sukayi gabad'aya sbd yanda yayi maganar.

Matar Amjad tace "kenan ka yarda Kuna da hali?eh amma *wasu mazan*.... ba wani komai haqurin d'a namiji sae an sami wani hali nasa da yake 6atawa matar sa rai bare zaman tare ai sa6ani yayi yawa a cikin sa sae anata haquri ne ake cin ma riba domin yau ba don haquri ba Allah bazan kawo ma abincin nan ba, Amjad take gaya ma hakan yayinda take dariya tace "nifa na d'aukawa kaina kawo ma abinci ba kai kasa ni ba amma duk ranar da uzuri ya kama ni nayi lettin kawo ma sae ka cika ni da masifa......naji amin afuwa dan Allah kin san matsalata duk yanda naji yunwa nan take ne ulcer ta ke tashi kuma kinsan yanda ulcer kemin kamar na mutu,no ba komai my dear ai kasan na fi kowa tsorata idan ulcer ka ta tashi bcs ko mutuwa kayi ni aka bari da takaba ba kowa ba,
shiyasa kullum roqona na mutu kafin kai.......no no gaskiya ni ya kamata na mutu kafin ke bcs idan kika mutu ai shikenan na tashi da aiki bazan qara yiwa kowa amfani ba.... hm zo zo muje Billyta kar zumar da suke nunawa junan su tasa su haifo 'ya' yan zuma yanzu abin al'ajabi ko ya same mu,,, kaji ka wai kwando kece wa rariya na yoyo, cewar Amjad kafin yake cewa
"kinga dear zo mubi sahun su bcs yau banda wani aiki da zai kaini dare da na sani ma baza kiyi wahalar kawo min abinci ba".
 Nan suka fita tare inda kowa ya shiga mota suka nufi hanyar gidajen su.

 Suna isa pinky ta cire kayan jikin ta ta zamo daga ita sae vest da d'an guntun wando Hakeem ya shigo sanye da singlet and boxer ya same ta ruf da ciki tana chat zuwa yayi close to her ya kwanta rairan yayinda ya d'ora qafa kan qafa yana mai kallon fuskar ta.
ajiye wayar tayi tare da kwanciya kan qirjin sa ta kai hannu kan sajen fuskar shi da ya soma taruwa tana d'an jan sirarin sumar a hankali ta yanda ba zai ji zafi ba,
hannun sa taji tsundum cikin vest in ta yana abinda ya saba yi a qirjin ta turo baki tayi tana kallon shi taja sumar sajen shi da qarfi har sae dai yayi qara inda hakan yasa ya fitar da hannun shi cikin vest in ta ba shiri yana murza sajen shi,
jaye hannun shi tayi tana ci gaba da murza mishi a hankali da wasa ya buge mata hannu yace ki daina min bana so,tukuna ma me  namiki? ba kai bane ko yaushe idan ina tare da kai sae kayi ta takura ni kan abokanan wasan ka, oh yayi kyau a kanshi ne kawai sae kace ba kaya na ba.....a'a gaskiya bana la6i ni kad'ai  nake da  abuna kar ka sake ta6a min, haka kika ce?eh, shi kenan da ga yau nima kar ki qara kwanciya kan jikina sbd na fahimci jikin nan nawa yana miki dad'in kwanciya ko yaushe kina maqale da ni,cikin ko in kula tace"ai wannan ba matsala bane amma dai bara nayi na qarshe,
nan ta rungumo shi sae kuma tayi saurin jaye wa  tana dariya sae kare qirjin ta take kar ya ta6o, murmushi yayi ya tallebeta cak tare da fad'in ai da kin daina kare qirjin ki sbd ba abinda zan miki  bacci ma nake so muje muyi " um um fa nasan halin ka Bobby kullum idan zamuyi bacci sae kayi ta takura ni kan abokanan wasan ka har bacci ya d'auke ni baka daina ba,
hancin ta ya lakato tare da fad'in" banda yau zan barki ki hutu har safe.
  Kaji shi kaman zai iya, dariya yayi Yace"Billyta kenan to zan miki qarya ne "
rufan asiri ni bance qarya kamin ba.

  Ta fad'i haka ne yayinda suka iso d'aki ya dire ta kan bed yaje ya rufe d'aki sannan ya rage hasken d'akin yaje ya kwanta yayinda Billy ta mirgino kan qirjin sa da ko yaushe take jin dad'in kwanciya akai sbd fad'in qirjin, shiru sukayi inda suke jiran bacci ya d'auke su,
Hakeem sae shafa bayan Billy yake a hankali kamar yanda Billy ke yawo da hannun ta kan qirjin shi.
  Da haka har tayi bacci nan Hakeem ya zare hannun ta a hankali da ke cikin vest in shi ya gyara mata kwanciya shima ya shiga bacci.

              *******
Sannu sannu lokaci ke ta tafiya inda yanzu cikin pinky yakai har wata shida.


Shiri take cikin sauri yayinda Hakeem ke tsaye yana jiran ta kan bikin su Feenah da Naini da zasu je.
    Yace"Billyta kinga mutane sae kira na ake tayi kuma ke gashi har yanzu shirin naki bai gadi qarewa  ba, yi haquri Bobby yanzu zan qarasa shirin,
 numfashi ya sauke ya duqa a hankali kan cikin ta da ya fara fitowa ya d'ora kiss akai yace " sorry my child ni zan tafi ku same ni a mota "nan ya tashi ya d'ora mata kiss kan kumatu yace"zan jiraki a mota" gyada mishi kai tayi yayinda take ci gaba da shiri.
  Tana gamawa ta tafi sauri sauri ta same shi a mota suka tafi.


Sun jima sosai da zuwa sae ga Billy ta dawo ita da Hajiya seema sae dai bata jira Hajiya seema ba,
ta shiga  6angaren su umma kan ta shiga wata ta tsaida ta  tace "da Allah pinky fa? nice pinky da wani abu ne, sae da ta kalli cikin Billy tace" no ba komai kawai ni qawar feenah ce ina so zanje event in da ake yi yau amma ban gane guri ba,, Eyyah wato ke qawar Feenah ce but ya akayi ba mu san juna ba,,, baza ki sanni ba bcs a kasuwa kawai abotar tamu ta had'u, ok haka ne bazan sanki ba gsky but muje daga ciki idan zan koma sae mu tafi tare.
    Nan suka shiga baquwar ta zauna Billy ta haura sama zuwa d'akin umma ta sami umma tana waya ta zauna tare da kwantar da kanta kan kafad'ar umma, umma na gama waya tace "umma yunwa nakeji ko da fresh milk a nan 6angaren sbd mu a namu 6angaren jiya da dare na qarasa shanye ta? Cabd'i sae dai kije ki bincika idan zaki samu sbd jiya da su Feenah suka kwana a nan ita suka bawa  qarfi,
cikin shagwa6a ta tashi tace" Allah yasa zan samu "
 Nan ta nufi fridge d'in dakin.

6angaren baquwar kuwa waya take tana dube dube kamar marar gaskiya tace" kinga Halima kamar ba abinci taxo nema ba fa bcs ta shiga daga ciki tace na jira ta ta fito mu tafi..... haba sau nawa zan gaya miki abinci taxo nema ina biye da ita a gurin bikin duk abinda take ina sane kawai kije cikin fridge ki sami fresh milk bcs ita ce favourite d'in ta sea ki zuba wannan garin maganin a ciki in yaso ki kama jiki ki bar gidan kafin su fito su riskeki nidai fatana Allah yasa seema ce zata bata fresh milk d'in da hannun ta bcs aikin zai fi kyau but ina kule tun can take nema mata abinda zata ci nasan baza a sami matsala ba ita zata nema mata ko wannan karon ,,,, to gashi kuwa Hajiya seema tayi zaman ta fa a mota bata fito ba har yanzu sae waya take "eh kiyi aikin ki kawai kuma idan ma fresh milk d'in suna da yawa kibi kowace ki saka......Duka fa? .... Eh man to wa yasan wacce zata d'auka a ciki kuma maganin ba kisa yake ba kawai za'a sha wahala wanda in Billy tasha  ko second d'aya yaron cikin ta ba zai qara ba zai mutu,
to kamar yanda yaron cikin ya mutu ba zai sake dawowa ba har abada haka auren seema zai mutu har abada kuma ba zata sake yin aure ba,,,
amma meyasa kike son sae Billy za'a bawa maganin?sbd ita kad'ai na sani mace mai ciki na wata shida bcs boka yace sae cikin wata shida ne zai yi aikin, just kawai kiyi sauri kimin aikina kizo na biyaki ladar ki.
 " ok to"
 Nan  ta tashi ta nufi fridge koda ta bud'e fresh milk kwali d'aya ta samu,
cikin hanzari ta zuba garin maganin ta rufe tana rufe fridge sae ga Hajiya seema ta shigo wanda yayi dai dai da saukowar pinky sae kukan shagwa6a take tana fad'in wai ni ina zan sami fresh milk a gidan nan"
ganin baquwa a gun fridge yasa Hajiya seema tace "yadai wani abu kike so? Eh wai ruwa ne na sha.... Billy da ta qaraso tace" Mtsw yi haquri ban baki ruwa ba na tafi but dan Allah a cikin fridge d'in ko akwai fresh milk ? Eh inaga kamar na ganta a ciki..... Hajiya seema tace" lallai bari muga kamar na hango ta kafin ta rufe fridge d'in,
nan ta bud'e ta d'aukowa Billy wacce ta buga ihun murna ta kar6i fresh milk a hannun Hajiya seema, baquwar tace "Pinky ni zan tafi bcs na kira feenah tayi min misalin gurin ina so naje kafin bikin yayi nisa, ok shikenan sae mun had'u.      
 Daga haka ta fita inda ta manta wayar ta kan seater ba tare da kowa ya lura ba har ta wuce.

Billy kuwa ta bud'e fresh milk zata kafa kwalin gabad'aya a bakin ta sae aka kar6e kwalin tare da cewa "ban fara ra'ayin d'an qaramin bakin nan ya qara girma ba ina cup da baza kisha da shi ba? cikin 6acin rai irin na shagwa6a ta kalli Hakeem wanda ya kar6e kwalin tace "meye haka Bobby ?
ai ke zan cewa meye haka kin baro gurin biki bayan kinsan ba irin bikin da zaki bar guri bane,, ai yanzu komawa zanyi bani fresh milk nasha tukun sae muje dama mama tace ita baza ta koma ba....no ajiye zancen fresh milk kizo muje sauri nake,kuka ta ajiye mai tace "nidai pls ka barni nasha tukun ....idan mun dawo ba,, ya fadi haka ne yayinda umma ta sauko, Billy ta kalli umma cikin kuka tace" umma wai ba zai bari na sha ba har sae mun dawo kuma yunwa nake ji kamar na mutu"

 Hava Hakeem ya tana jin yunwa zaka ce sae kun dawo bayan yunwar ce ta maida ta gida....amma umma shine zata ajiye min kuka bata min bayani ba bayan tasan bana son kukan nan da takeyi kuma yunwa sae kace ba abinci a can duk ina kalolin abincin da kika baro? Bobby bana ra'ayin ko d'aya a cikin su kuma ba fresh milk a gurin....Mtsw ya buga guntun tsaki yaja hannun ta yace"zo muje kya sha ta a cikin mota, qunquni ta shiga yi ita baza ma ta sha ba ko yunwa zata kashe ta kuwa, Hakeem yaji sak me take fad'a yayi shiru kamar bai ji ta ba.
 Da suka shiga mota ya bata fresh milk taqi kar6a nan ya ajiye mata ita kan jikin ta yaja motar cikin 6acin rai.
   Suna isa ta fita tun mota bata qarasa tsayi ba ta kuma jefar da fresh milk kan seat ta wuce kallon ta kawai Hakeem yayi shima ya fito motar ba tare da ya d'auko mata fresh milk in ba.


Tun six sae guraren qarfe tara na dare suka dawo inda har yanzu fishi Billy keyi.
   Sun d'an jima da dawowa ne Hakeem yaje d'akin  Billy ya samu har tayi wanka tana shirin kwanciya zama yayi kusa da ita yana rarrashin ta har ya samu ta haqura suka je d'akin shi.
  Suna shiga d'aki ya bud'e fridge ya d'auko fresh milk da cup yaje ya zauna kusa da ita ya tsiyaya mata a cup yace "ungo kisha tunda muka shigo na sanya miki ita a fridge shine har ta d'an soma yin sanyi,
ba musu ta kar6a takai kan lips kenan taji bata yi sanyi a yanda take so ba cikin fushi ta ajiye cup tace" tun d'azu da ace ka barni nasha da zan fi jin dad'in ta amma sae da ta rage sanyi zaka wani ce nasha,
Tissue ya zaro ya goge mata lips in ta dake dauke da d'igon fresh milk yace "yi haquri bari na sanya miki qanqara tayi sanyi sae kisha kinji" ba ta ce komai ba sae kwanciya tayi kan gadon tana kuka mai cike da shagwa6a,,
Nan Hakeem yaje ya fashe qanqara ya saka mata sae da ya kwatan ci tayi sanyi yace " kukan ya isa haka tashi kisha yanzu tayi dai dai yanda kike so kinji "
nan ta tashi da mazarin ta sbd yunwa take ji sosai,
babyn cikin ta duk ya hana ta saqat sae motsi yake,
"jawota yayi jikin shi zai fara bata yace" bari dai nasha tukun naji idan tayi sanyi yanda kike so kar kiji ba dai dai ba ki ajiye min wani sabon kuka,
nan ya kai cup a bakin sa ya kur6a yace "wow tayi sanyi yanda kike so" oya bud'e bakin ki kisha " nan ta bud'e bakin ta bai riga ya bata ba wani irin tari yazo mishi ba shiri ya ajiye cup ya fara tari har da su zamewa kan gado duk Billy ta rikice ta durqusa kusa da shi tana murza mishi bayan shi sae sannu take mishi.
Ganin tana qoqarin mishi kuka ya samu da qyar ya tsaida tarin yace " is ok ta d'an sarqe ni ne kar kiyi kuka kinji, ungo sha kar yunwa ta miki yawa but take care kema kar ta sarqe ki kinji, gyada mishi kai tayi ya tashi ya nufi toilet cikin sauri sbd tarin da ke qoqarin sake zo mishi,
da shigar shi ya kunna famfo don kar taji sautin tarin da yake wanda kan tsananin wahala har wani kalar amai ya fara yi mara kyan gani.
  Billy kuwa sae da ta qara qanqara tayi zaune tare da kai cup a bakin ta.

*Billy giro 😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 8:40 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [9/9/2016]

 *👛BILLY PINKY DURLING 👛*




*Na Billy giro 😊*




*Page*

*👛75&76👛*
Bata daina aman ba sae da ta amaye abinda taci kaf nan wani irin jiri ya d'ebeta ta tafi suuuu zata fad'i kwance a gurin.
  Hakeem yayi hanzarin jawo ta ta fad'a jikin shi,sae kallon ta yake kamar wanda zai mata kuka duk ta bashi tausayi haka ma Naini da Feenah da ke gurin duk ta basu tausayi.
  Hakeem ya kalle su cikin matsananciyar  damuwa yace "pls Naini kira min Amjad a waya yazo ya duba min ita,
nd u Feenah pls je kira min umma, ba musu Feenah ta tashi ta fita Naini kuma ya shiga dialing number d'in Amjad shi kuma Hakeem ya d'auki Billy cak ya haura da ita sama nan Baraka taxo zata gyra gurin.

Hakeem na shiga da ita d'aki ya cire mata rigar jikin ta ya tafi da ita toilet ya watsa mata ruwa ya mata brush suka fita, suka sami umma tana jiran fitowar su ajiye Billy yayi kan bed wacce taje kan jikin umma tana wani galaibataccen kuka kan cikin ta da har yanzu masifar ciwo yake mata.
  Umma ta kalli Hakeem wanda ke kallon Billy yana ji kamar ya maida ciwon kan jikin shi,
  tace "Hakeem tun yaushe ne Billy take fama da rashin lafiya har tazo ta galabaita haka baka sanar da ni ba? 2 days but abin bai yi yawa ba sae yau,
Amma gsky  umma na tsorata idan ba farfesun kifin da taci bane yake d'auke da wani abu, kamar ya?bcs tana kan cin farfesun kifi kawai ta tashi tana amai..... kar ka damu indai wannan ne, yanzu sanya mata riga Amjad zai shigo ya duba ta.
   Nan ya nemo riga ya saka mata aka bawa Amjad damar shigowa yayi en gwaje gwajen sa kan pinky ya kammala yace "MashaAllah Hakeem sae ka kwantar da hankalin ka domin wannan abin farin ciki ne ya samu sae dai nace congratulation u are going to be a father....... bakin sa ya bud'e dariya ko murmushi ya rasa wanda zai yi ya nuna Amjad tare da fad'in tsakanin ka da Allah!?eh tabbas kuwa juna biyu ne da Billy.

    Kai a bar zancen kawai domin murnar da Hakeem ya shiga ta wuce a bar misali kan tsananin murna bai san lokacin da ya jawo pinky yana kai mata hot! hot! kiss ta koina sae tambayar ta yake da gaske Billyta,
da gaske na kusa zama Abba da gaske I'm going to be a father at year of 2017!
"ya Rahman! "
ya fad'i hakane yayinda ya zame jikin sa ya durqusa kan guiwoyin sa ya d'aga hannyen sa sama yana godewa mai duka mai komai.

Hm! a yanda ya shiga gode masa kyace shekara ashirin yayi yana neman haifuwa bai samu ba sae yanzu.

Cikin farin ciki da dariya umma tace" Hakeem ya isa haka mana .... "no umma ai godiya bata yawa ko Billyta?
  Ya fad'i haka ne yayinda ya riqo hannyen Billy yana murmushi ita ma murmushin ta mishi wanda yayi dai dai da shigowar Naini da Feenah wad'an da jin sautin yanda Hakeem ke zabgawa ubangiji godiya yasa suka kamo jiki suka shigo,
nan aka sanar da su farin cikin da ake ciki inda sukayi matuqar farin ciki da jin zancen har Naini ya bawa Hakeem hannu yana mishi congratulation Feenah kuma zama tayi kusa da Billy tare da riqo hannyen ta tana taya ta murna da haka suka  qaraci farin cikin su inda Amjad ya rubuta irin magungunan da zata riqa sha da kuma irin abincin da zata riqa ci masu qara jini da kuma qara lafiya.
   Wannan kenan.

 Abincin masu ciki ne kala kala da 'ya' yan fruits ba adadi jere a kan dining table wanda ya cika maqil tamkar mutane goma ne zasu ci abincin, yayinda Billy keta zubawa Hakeem kukan shagwa6a ita baza ta ci ko d'aya ba sbd tsoron kar taci taje tayi amai dmn ko kad'an bata son tuna wahalar aman da tayi a d'azu shiyasa take gudun sake cin wani abu.
  Ba irin rarrashin da Hakeem bai yi ba amma taqi ci yace "Billyta kalle ni nan" a hankali ta d'ago kan qirjin sa tana kallon cikin idonshi inda ta hango damuwa fall a cikin su.
   Nan ya had'e tafukan hannayen sa yace "don Allah Billyta kici wani abu kinji" le6ace bakin ta tayi xuwa kuka tace "Bobby um um" kina so nayi fishi da ke? saurin girgiza kanta tayi d'auke da hawaye tap a idon ta yace "to idan baki ci ba zanyi fushi da ke kuma bazan qara miki magana ba" ta nuna kanta da yatsa tace "ni d'in ? yace" eh man ba kinqi kici abinci ba kin bar min Baby da yunwa "um um ni bana so kayi fishi da ni ina gudun kar nayi amai ne shiyasa bana so naci,baza kiyi amai ba inshaAllah, nan ya shafo cikin ta yace"ai nasan kina so babyn mu yayi qiba baza kiso ki haifo mana shi a ramamme ba ko? gyad'a mai kai tayi tare da fad'in" eh " yauwa tawan to share hawayen ki kici abinci, ba musu ta share hawayen ta yasa handkerchief ya qara share mata yace" to nuna min me kike so a nan, nan ta shiga rarraba ido kan ko wane abinci nan faten wake ne wanda yaji ganyen ogun da kifi nan kuma ganyen zogale ne da aka soya  da qwai mai d'auke da kayan lambun da aka soya sama sama  sae qamshi ke tashi,
nan kuma farfesun kaji nan kuma na en ciki nan kuma spaghetti ce wacce akayi ta ruwa ruwa taji ganyen alanyahu da wake da hantar rago sae kuma sakwara tayi laud'i da taushi har ta gaji da miyar stew wacce taji naman rago, nan ta koma kan fruits shammal, gwanda, Apple, grapes, Banana, orange, pineapple, guava,watermelon,whatever haka ta qaraci kallon su har zuwa drinks ta juyo ta kalli Hakeem fuska a shagwa6e tace "Bobby idan naci bazan yi amai ba? lumshe idon shi yayi tare da fad'in "inshaAllah then  nuna min za6in ki"
nan ta nuna mishi kankana ya d'auko slice d'aya zai kai a bakin ta sae fargaba take kar tayi amai ta riqo hannu shi tare da bud'e bakin ta a hankali suka saka kankanar a tare kallon shi take tana shan kankanar tana gama shan slice d'in tayi saurin rufe bakin ta ta sauka kan jikin sa tana yunqurin amai se duk Hakeem ya shiga damuwa yayi saurin zamewa kan kujera ya durqusa tare da dafa ta  yace "pls Billyta kar kiyi amai dan Allah"
   Yunqurin aman kuwa sae zo mata yake amma ta kasa yin amai jinginawa tayi a jikin sa tana sauke numfashi, Hakeem ya dauko ruwa zai bata ta dakatar da shi had'e da girgiza kanta ta samu da qyar tace "Bobby cikina yana min ciwo sosai" sannu ya shiga yi mata ba adadi sannan ya kama ta suka koma kan dining ya zuba mata fresh milk ya samu da qyar ta kar6a ta kur6a kad'an ta kauda kai ganin bata yi amai ba ya qara lalla6a ta yaci gaba da bata,
bata wani sha da yawa ba tace ta ishe ta.
  Kallon abincin kan dining yayi yace "to me kike son ci cikin abinci?kukan shagwa6a ta shiga yi mishi tana yarfi da hannu tace" Bobby cikina ke min ciwo dan Allah ka daina zancen abinci "kiyi haquri kici ko kad'an ne sae kisha magani kiyi bacci kinji" uhm uhm Bobby kayi haquri bazan iya cin komai ba,
cikin damuwa yake kallon ta ya rasa me zai ce mata ya dai samu taci ko kad'an ne.
   Ita ma Billy kallon fuskar shi take sae duk taji ba dad'i ganin yanda ya shiga damuwa ta share hawayen ta tace"am sorry Bobby zanci abincin "da murnar sa yace to me kike so? faten wake nake so,
nan ya zuba mata ya shiga bata sae dad'i yake ji ganin yanda take cin abinci ita kuma tana cin abincin ne don kawai ta faranta mishi rai sae da tace ya ishe ta sannan ya daina bata ya d'auko ruwa da magani ya bata tasha sannan suka koma d'aki ta kwanta ya rufa mata blanket sae kallon shi take yana gyara mata sumar kanta tace "thank u" yayi murmushi hade da bata kiss kan goshin ta yace " welcome"

Sae da tayi bacci yaje downstairs ya d'obo sakwara da miyar stew ya zauna kan sofa inda yake facing d'inta yana ci wanda komai qanqantar motsin da tayi sae ya d'ago ya kalle ta da haka har ya kammala cin abinci .

*Billy giro 😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 8:41 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [9/10, 10:29 AM] Billy giro😊:
*👛BILLY PINKY DURLING 👛*




*Na Billy giro 😊*



*page*
     *👛77&78👛*
Ta jima sosai tana bacci yayinda Hakeem yake kwance kan gadon yana kula da duk wani motsi nata.
   A hankali ta shiga motsawa tana juyi tare da dafe cikinta ta fara fitar da sautin kuka kad'an kad'an,
nan Hakeem ya matso kusa da ita yana tambayar abinda ke damun ta bata iya ce mishi komai ba sbd yawun da ya cika mata baki inda duk cikin ta ya mirda ne kesa yawun ya taru,
zare jikin ta tayi ta tafi toilet da sauri tana isa ta shiga kwara amai ta samu da qyar ya tsaya mata , Hakeem da ke riqe da ita ya wanke mata baki ya kuma wanke gurin,
da qyar take iya takawa bata iya miqewa da kyau kan ciwon ciki,
sae kuka take mai cike da wahala,
Hakeem sae faman rarrashin ta yake ya zaro waya ya kira Amjad wanda bai wani jima ba yazo.
cikin damuwa Hakeem yake sanar da shi yanda ciwon cikin ke wahalar da ita, Amjad yace "kayi haquri Hakeem kalar laulayin ta ne yazo da hakan kuma ba a iya magance shi sae idan Allah ne ya yaye mata but zan mata wata allura na kuma rubuta mata wasu magunguna inshaAllah abin zai d'an rage mata har ta samu ta kai lokacin da laulayin zai rage mata.
    Nan Amjad ya shirya allura Billy sae kuka take tana roqon kar a mata inda ta shiga qoqarin qwatar kanta ta samu ta guje ma allurar,
ba a son ransa ba ya matse ta aka mata allura kuka take sosai yana murza mata bayan ta,
 kai tsaye ta shiga kwara mishi wani irin amai duk tabi ta 6ata jikin su tana qoqarin somewa inda ko qaqa Hakeem yaso yayi kuka ko zai ji sauqin damuwar da ya shiga akan halin da yake ganin pinky ciki amma haka ya dake yana ta hana kanshi domin kukan sae qoqarin zo mishi yake wanda duk da haka sae da  idanun sa suka cika tap da qwallah,
ya kalli Billy dake kan jikin shi yaga kwata kwata bata motsi duk ya rud'ewa Amjad yana fad'in Amjad na shiga uku! bata motsi fa dan Allah duba min Billyta kar ta mutu.....calm down suma ne tayi nan suka watsa mata ruwa taja numfashi da qarfi ta kuma ci gaba da kwara amai sae kace wacce zata amaye en hajin ta duk Hakeem ya qara rikicewa yana qoqarin yiwa Amjad kuka, Amjad yace "kayi haquri Hakeem allurar ce ke suffering d'in ta haka but daga haka inshaAllah wahalar zata rage mata,
nan ya rubuta mishi magunguna tare da fad'in tunda yanzu aman ya tsaya mata kayi sauri ka bata wani abu taci kafin tayi bacci sbd allurar tana sa bacci sosai ya fad'i haka ne sannan ya fita tare da fad'in Allah sauwaqe.
Nan Hakeem ya tashi yaje toilet ya wanke musu jikin su sannan ya gyara gurin da tayi amai tsaf,
ya dawo kan Billy wacce ke kwance d'aure da towel,
zare towel d'in yayi ya barta da pant ya d'auko half vest da guntun wando iya cinya ya saka mata sae kallon cikin ta yake da yayi mugun lafewa,
en guntayen hawayen shi ya share yayinda ya kalli Billy wacce ko qaramin yatsan ta bata da qarfin motsawa.
   Fresh milk ya debo wanda ko kur6i d'aya da qyar ya samu ta hadi'ye shi yayi 2 ta bud'e bakin ta domin ta qara sha amma taqi har bacci yayi awon gaba da ita.


Tun bayan la'asar da tayi bacci sae goman dare ta farka ta bud'e idon ta inda ta had'a ido da Hakeem wanda ke rungume da ita  , wanka ta buqaci tayi yaje ya mata da kanshi ya samu ya bata wani abu taci ta samu ta ranka sallolin da ake binta amma duk da zaune tayi su sbd ba qarfin jiki.
   
  Har ukkun dare basuyi bacci ba,
ba don komai sae don Billy bata jin bacci shi kuma Hakeem sosai yake jinsa amma haka ya dake ya hana kanshi sbd baya so yayi bacci Billy ta buqaci wani abu.
  Billy ta lura da irin yanda yake jin bacci hakan yasa ta qara lafewa jikin sa ta tsiri baccin qarya nan  Hakeem ya samu yayi bacci ita ma daga baccin qarya na gasken ya zo mata.


Washe gari sae da aka yi mata qarin ruwa har gora biyu sbd bata da qarfin jiki ko kad'an da ta tashi tsaye jiri ne ke d'ibar ta ta fad'i amma tunda aka  sa mata gora biyu taji jikin ta yayi dama.

A nan gidan feenah ta yini sae fira suke ita da Billy wacce ta d'an fara jin sauqi.
  Hakeem kuma yana falo shi kad'ai sae rubuce rubuce yake yana lissafi kan wani aiki da Abba ya sashi.
   Yana cikin aikin ne ya hango Billy ita da feenah zasu sauko nan ya tashi ya qarasa gurin su ya riqo hannun Billy zai tallabe ta tace "eyyah Bobby wai don ka dauke ni ne kazo ai da ka yi zaman ka bcs yanzu ina d'an jin qarfi har ma ina iya tafiya" kin tabbatar baza ki fad'i ba?lumshe idon ta tayi tare da fad'in inshaAllah yace "duk da hakan dai bazan yi zuwan banza ba nan ya d'auke ta cak inda Billy ta sakad'o hannuwan ta kan wuyan shi tana mishi murmushi shima haka,
Feenah sae kallon su take cike da sha'awa har suka sauko ya ajiye ta bakin qofa yace" yauwa kinga yanzu ko faduwa kikayi bazan tsorata irin upstairs ba, Kuma na ajiye ki ne don na fahimci kamar kina son takawa da kanki, murmushi ta mishi tace "thank u" sannan taja hannun feenah suka je ta rakata ta shiga mota ta wuce.
   Da qyar taga ta dawo  kan jirin da take ji, tana shigowa ta fad'a kan jikin Hakeem tana d'an sauke numfashi da kulawa ya kalle ta yace "kin gani ko Billyta tafiyar ta wahal da ke,ko har yanzu cikin ki na ciwo ne ?um um kad'an ya keyi,, nan yayi shiru yayinda ta qara gyara kwanciyar ta kan jikin shi, yaci gaba da aikin shi sae wasa take da buttons d'in rigar shi  ta bud'e ta rufe haka tayi ta yi har ta bud'e su gabad'aya inda ta shiga  shafar qirjin sa da ya kasance very smooth mai cike da sheqi .
  A hankali ya dakata da aikin da yake yana kallon d'an yatsan ta da take kewaye ramen cibiyar sa dashi,
hannun sa yakai kan qugun ta ya qara manna ta a qirjin sa yana d'aga rigar ta a hankali inda ta bayan qugun ta take jin yana yawo da yatsan shi har ya zagayo gun cibiyar ta yana zagaye cibiyar cikin wani irin salo, numfashi ne yazo mata a hankali sannan ta rumtse ido gam tare da jan numfashin ta hakan yasa cikin ta ya qara mannewa a jikin ta.
  Qara qanqame shi tayi tace "Bobby stop it" nan ya d'ago yana kallon d'an qaramin bakin ta yaje a hankalin ya tsotsi bakin sannan ya sake kallon ta yaga still bata bud'e idon ta ba, sae hannun ta takai kan hannun shi da yake shafa cikin ta,
yace " Billyta bud'e idon ki mana" tace "um um tare da maqale kafad'a yace" meyasa? bude idon ta tayi tare da turo baki ta nuna shi da yatsa cikin sigar  yarinta, sannan tace "ba kai bane",
cizo mara zafi yakai mata kan bakin ta da ta turo yace "ai ke kika fara har kika sa nayi kuskure a lissafin da nake shiyasa nayi punishing d'in ki domin kinsa aiki na ya dawo qasa" da kulawa ta kalle shi yayinda ta d'auki takardun da yake aiki kansu tace "Bobby da gaske? Allah kuwa.... Oh no wlh Allah ba don kaji wani abu na maka abun ba,dan Allah kayi haquri,,, ni bazan haqura ba sai kin min kiss guda goma kuma ni zan nuna gurin da nake so da kai na, olryt nuna min?nan ya shiga nuna mata ita kuwa sae banka mai kiss take duk inda yace,
 da ta kammala ya rad'a mata wata magana a kunne wacce tasa ta tashi tana dariya ta rufe fuskar ta tace "Allah bazan iya ba, ok zo zauna dama wasa nake miki nan ta zauna ta taya shi sake lissafin da yayi kuskure Bayan sun kammala ya shafo cikin ta yace" amma maman Babyna tana jin yunwa ko? Allah kuwa yunwa nake ji, ta fad'i haka ne yayinda take taya shi shafar cikin ta,
nan ya d'aga ta suka je kan dining suka ci abinci suna gamawa Hakeem ya wuce masallaci sbd lokacin sallar isha'i yayi sae da ya jima kafin yake dawowa ya tafi d'akin Pinky wacce ta fito daga gurin wanka kenan jin shigowar shi yasa tayi saurin komawa tana leqen shi, yace "Billyta mene ne? ba komai a jikina pls i need towel.... hhhh ya haka keda ke cewa na daina fitowa ba kaya a jikina amma shine kika fara,,, da towel na shiga but na shiga ne a gaggauce sbd aman da yazo min sae duk ya 6ata min towel shine na saka a washing machine na wanke,,, Hakeem ya d'auko towel cikin er damuwa ya bata ta daura sannan ta fito ya riqo hannun ta suka zauna yasa qaramin towel yana tsane mata gashin kanta da ta wanke yace "Billyta ina ce aman bai wahal da ke sosai ba?gyad'a mishi kai tayi tace" da sauki gsky ba kamar sauran ba "that's gud be patient kinji" inshaAllah i will and u pls ka rage sa damuwa a ranka, inshaAllah Billyta.
 Nan ya fara cire buttons d'in rigar shi a cewar  zai yi wanka nan ta taya shi ya cire rigar ta shiga zare mai belt yayinda ta kalle shi ta wani marairai ce fuska tace "pls Bobby ina neman wata alfarma don Allah wannan karon kar kace a'a,,, mene ne Billyta?......
nan ta gaya mishi ya kalle ta sau d'aya ya kauda kai yace" gasky kiyi haquri hakan ba zai samu ba,,, kallon sa tayi kamar zata yi kuka ya tashi ya wuce toilet cike da shagwa6a ta bishi toilet tana mishi kuka,wata uwar tsawa ya daka mata yace " sau nawa zan ce ki daina min wannan maganar ne!
Please go out!! i said go out!
 ba shiri ta fita  taje ta fad'a ruf da ciki kan bed tana rusar kuka.

*Billy giro 😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 8:42 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [13/9/2016 ]

*👛BILLY PINKY DURLING 👛*



*Na Billy giro 😊*


*Page*
      *👛79&80👛*
Ya jima kafin yake fitowa ya samu har lokacin Billy kuka take,
yayi tsaye yana kallon ta.

Cikin fushi ta tashi ta fita ya bita da ido yayinda ya qara jin kansa da 6acin rai har yana jin kamar ya bita yayi ta yi mata fad'a,
sae dai kuma da ya tuna cewa tunanin shi da nata ba d'aya bane kuma shine babba shine ya kamata ya sauko yaje ya rarrashe ta.
 Nan ya bita falo  ya samu ta had'e kai da guiwa tana faman ci gaba da kuka,
ya zauna kusa da ita tare da dafa ta tayi saurin jaye mishi hannu, inda ya shiga magana cikin muryar lallashi yace " Billyta ki daina kukan nan haka ba kya gudun ciwon kai ne,
gashi kuma kinsan ba kya da isassar lafiya"
ya fadi haka ne yayinda ya jawota jikin sa zai share mata hawaye,
taso ta fizge jikin ta daga nashi sbd ya 6ata mata rai kan tsawar da ya daka mata,
sae kuma taga in tayi hakan ba riba gara ta haqura ta kuma lalla6a shi ko zai yarda da abin da take so.
Nan ta qara lafewa  a jikin shi ta d'ago da idanun ta da suka cike tap da qwallah tace" please Bobby ka taya ni yaqin nan ko Abba zai amince ya maida mama tunda tayi nadamar abin da ta aikata kuma tun lokacin cikin aiko masa saqon ban haquri take,
kauda kansa yayi domin ko kad'an baya son tana mishi maganar mama kan illata Billy da taso tayi sae duk yaji ya tsane ta har baya son yaji an ambace sunan ta, Billy ta juyo da fuskar sa wacce ke d'auke da damuwa tace " please Bobby dan Allah dai"
  Kallon ta yayi yayinda zuciyar shi ke ta ingiza shi kan ya daka mata tsawar da ko da kuskure baza ta qara tuntu6ar sa da wannan zancen ba, amma ganin yanda take ta lalla6a shi yasa ya danne duk wani abu da yake ji ya shiga share mata hawayen  da suka gangaro sannan yace" naji Billyta zan yiwa Abba magana "
sosai taji dad'i har tana mishi godiya nan yaja hannun ta suka haura sama domin sanya tufafi kasancewar kowanen su towel ne dashi.



After 1 week

8:30pm

Hakeem ne tsaye a jikin mirror ya fito daga wanka yana goge sumar kanshi da d'an qaramin towel.
 Billy ta shigo d'akin sanye da er fincikar rigar bacci handless iya cinye yayinda ake hango rabin mamanta a waje sbd yanayin style d'in wuyan rigar.

A hankali ta rungumo Hakeem ta baya inda suke hango juna ta jikin mirror, murmushi suka sakar wa junan su,sannan ya zagayo da ita ya xaunar da ita kan cinyar shi, ya kai d'an yatsan shi kan tsagin mammanta yana yawo da shi,
cikin hikima Billy ta jaye hannun shi sbd tasan in ya fara wasa da abokan wasan shi ba daina wa zai yi ba.
    Kiss ya dorawa qirjin kafin
Billy ke cewa"godiya nake my soldier man naji dad'in yanda Abba ya haqura ya maida mama but pls gobe zaka bar ni naje gidan?

Shiru ya mata yayinda murmushin fuskar shi ya 6ace,
ya Kalle ta sau d'aya ya kauda kai,
nan wayar shi tayi qara yace " d'auko min waya ta " wanda kafin yace hakan tayi niyar d'auko mishi wayar sbd tana tunanin Abban ta ne ya kira bcs tana cikin waya da shi ne cajin wayar ta ya qare sea tayo d'akin Hakeem.
    Da hanzari ta tafi d'auko wayar tana fad'in "yeah Allah yasa Abbana ne" .......qara ta saki sbd fad'uwar da tayi kan wani jiri da ya d'ebe ta.
   Ba shiri Hakeem ya jefar da d'an qaramin towel d'in da ke hannun shi yana isa ya tayar da ita ta fada kan qirjin sa da qarfi duk tabi ta qanqame shi tana kuka kamar wacce ta tsorata
hakan yasa Hakeem ya d'ago fuskar ta tare da fad"in "Billyta mene ne, me ya kayar da ke?tace" wani irin jiri ne ya d'ebe ni har naga d'akin yana juya min kamar zai fad'o min" oh no sorry but a u ok?  "am ok" nan ya kwantar da kanta a qirjin shi yana mata sannu shafo cikin ta yaji tayi yayi saurin kallon ta tare da shafo cikin yace " wani abu ya sami babyn mu ne? girgiza kanta tayi tace" um um ba komai.....no tashi muje asibiti a duba bcs hankali na yafi kwanciya da hakan nan suka shirya sae asibiti bayan an gama duba ta Amjad yace "fad'uwar da tayi bai illata babyn ba amma ta rage dogon motsi sosai sbd hakan kesa taji jiri ya d'ebe ta kai tsaye kuma dama ba a cika son mai ciki na fizgar jikin ta ba, har dai ga mai sabon ciki then ga wasu magunguna da zan rubuta ma sea ka siya mata su ta riqa sha nan Hakeem ya kar6i takarda tare da sauke ajiyar zuciya yayi ma Amjad godiya kafin yake riqo hannun Billy yace "muje"

Har suna batun fita Hakeem ya juyo ya kalli Amjad da ba'a yace " doctor ko har da tafiya kar na sake bari tayi na riqa d'aukar ta..... Amjad yayi dariya yace" Baban soyayya to ko haka ne ai baza ka iya ba.... wa ya gaya ma Billyta ce fa,i know amma zai maka wahala..... to wane aikin wahala ne banyi ba nida nayi soja..... hehe ai ba zancen soja bane maza ne basu da tabbas sae kun fara d'and'anawa mutum dad'i kai tsaye ku daina koda hakan baya wahal da ku kuwa, Hakeem ya kalli matar Amjad wacce shigowar ta kenan tayi magana.

yace " wasu mazan dai don ni bana d'aya daga cikin su ko Billyta? hm Bobby kenan  a bar zancen kawai....gara da kika ce haka domin yanzu baza ki gane halin d'a namiji ba sae rayuwa taci gaba inda ke zakiyi ta haquri kina danne zuciyar ki ki samu ku zauna lafiya tare da fatar kar hawan jini ya kama ki.......a'a fa kar ki tsora ta min Billyta,wlh Allah ina sonta bazan so na nuna mata halin d'a namiji ba.....dariya sukayi gabad'aya sbd yanda yayi maganar.

Matar Amjad tace "kenan ka yarda Kuna da hali?eh amma *wasu mazan*.... ba wani komai haqurin d'a namiji sae an sami wani hali nasa da yake 6atawa matar sa rai bare zaman tare ai sa6ani yayi yawa a cikin sa sae anata haquri ne ake cin ma riba domin yau ba don haquri ba Allah bazan kawo ma abincin nan ba, Amjad take gaya ma hakan yayinda take dariya tace "nifa na d'aukawa kaina kawo ma abinci ba kai kasa ni ba amma duk ranar da uzuri ya kama ni nayi lettin kawo ma sae ka cika ni da masifa......naji amin afuwa dan Allah kin san matsalata duk yanda naji yunwa nan take ne ulcer ta ke tashi kuma kinsan yanda ulcer kemin kamar na mutu,no ba komai my dear ai kasan na fi kowa tsorata idan ulcer ka ta tashi bcs ko mutuwa kayi ni aka bari da takaba ba kowa ba,
shiyasa kullum roqona na mutu kafin kai.......no no gaskiya ni ya kamata na mutu kafin ke bcs idan kika mutu ai shikenan na tashi da aiki bazan qara yiwa kowa amfani ba.... hm zo zo muje Billyta kar zumar da suke nunawa junan su tasa su haifo 'ya' yan zuma yanzu abin al'ajabi ko ya same mu,,, kaji ka wai kwando kece wa rariya na yoyo, cewar Amjad kafin yake cewa
"kinga dear zo mubi sahun su bcs yau banda wani aiki da zai kaini dare da na sani ma baza kiyi wahalar kawo min abinci ba".
 Nan suka fita tare inda kowa ya shiga mota suka nufi hanyar gidajen su.

 Suna isa pinky ta cire kayan jikin ta ta zamo daga ita sae vest da d'an guntun wando Hakeem ya shigo sanye da singlet and boxer ya same ta ruf da ciki tana chat zuwa yayi close to her ya kwanta rairan yayinda ya d'ora qafa kan qafa yana mai kallon fuskar ta.
ajiye wayar tayi tare da kwanciya kan qirjin sa ta kai hannu kan sajen fuskar shi da ya soma taruwa tana d'an jan sirarin sumar a hankali ta yanda ba zai ji zafi ba,
hannun sa taji tsundum cikin vest in ta yana abinda ya saba yi a qirjin ta turo baki tayi tana kallon shi taja sumar sajen shi da qarfi har sae dai yayi qara inda hakan yasa ya fitar da hannun shi cikin vest in ta ba shiri yana murza sajen shi,
jaye hannun shi tayi tana ci gaba da murza mishi a hankali da wasa ya buge mata hannu yace ki daina min bana so,tukuna ma me  namiki? ba kai bane ko yaushe idan ina tare da kai sae kayi ta takura ni kan abokanan wasan ka, oh yayi kyau a kanshi ne kawai sae kace ba kaya na ba.....a'a gaskiya bana la6i ni kad'ai  nake da  abuna kar ka sake ta6a min, haka kika ce?eh, shi kenan da ga yau nima kar ki qara kwanciya kan jikina sbd na fahimci jikin nan nawa yana miki dad'in kwanciya ko yaushe kina maqale da ni,cikin ko in kula tace"ai wannan ba matsala bane amma dai bara nayi na qarshe,
nan ta rungumo shi sae kuma tayi saurin jaye wa  tana dariya sae kare qirjin ta take kar ya ta6o, murmushi yayi ya tallebeta cak tare da fad'in ai da kin daina kare qirjin ki sbd ba abinda zan miki  bacci ma nake so muje muyi " um um fa nasan halin ka Bobby kullum idan zamuyi bacci sae kayi ta takura ni kan abokanan wasan ka har bacci ya d'auke ni baka daina ba,
hancin ta ya lakato tare da fad'in" banda yau zan barki ki hutu har safe.
  Kaji shi kaman zai iya, dariya yayi Yace"Billyta kenan to zan miki qarya ne "
rufan asiri ni bance qarya kamin ba.

  Ta fad'i haka ne yayinda suka iso d'aki ya dire ta kan bed yaje ya rufe d'aki sannan ya rage hasken d'akin yaje ya kwanta yayinda Billy ta mirgino kan qirjin sa da ko yaushe take jin dad'in kwanciya akai sbd fad'in qirjin, shiru sukayi inda suke jiran bacci ya d'auke su,
Hakeem sae shafa bayan Billy yake a hankali kamar yanda Billy ke yawo da hannun ta kan qirjin shi.
  Da haka har tayi bacci nan Hakeem ya zare hannun ta a hankali da ke cikin vest in shi ya gyara mata kwanciya shima ya shiga bacci.

              *******
Sannu sannu lokaci ke ta tafiya inda yanzu cikin pinky yakai har wata shida.


Shiri take cikin sauri yayinda Hakeem ke tsaye yana jiran ta kan bikin su Feenah da Naini da zasu je.
    Yace"Billyta kinga mutane sae kira na ake tayi kuma ke gashi har yanzu shirin naki bai gadi qarewa  ba, yi haquri Bobby yanzu zan qarasa shirin,
 numfashi ya sauke ya duqa a hankali kan cikin ta da ya fara fitowa ya d'ora kiss akai yace " sorry my child ni zan tafi ku same ni a mota "nan ya tashi ya d'ora mata kiss kan kumatu yace"zan jiraki a mota" gyada mishi kai tayi yayinda take ci gaba da shiri.
  Tana gamawa ta tafi sauri sauri ta same shi a mota suka tafi.


Sun jima sosai da zuwa sae ga Billy ta dawo ita da Hajiya seema sae dai bata jira Hajiya seema ba,
ta shiga  6angaren su umma kan ta shiga wata ta tsaida ta  tace "da Allah pinky fa? nice pinky da wani abu ne, sae da ta kalli cikin Billy tace" no ba komai kawai ni qawar feenah ce ina so zanje event in da ake yi yau amma ban gane guri ba,, Eyyah wato ke qawar Feenah ce but ya akayi ba mu san juna ba,,, baza ki sanni ba bcs a kasuwa kawai abotar tamu ta had'u, ok haka ne bazan sanki ba gsky but muje daga ciki idan zan koma sae mu tafi tare.
    Nan suka shiga baquwar ta zauna Billy ta haura sama zuwa d'akin umma ta sami umma tana waya ta zauna tare da kwantar da kanta kan kafad'ar umma, umma na gama waya tace "umma yunwa nakeji ko da fresh milk a nan 6angaren sbd mu a namu 6angaren jiya da dare na qarasa shanye ta? Cabd'i sae dai kije ki bincika idan zaki samu sbd jiya da su Feenah suka kwana a nan ita suka bawa  qarfi,
cikin shagwa6a ta tashi tace" Allah yasa zan samu "
 Nan ta nufi fridge d'in dakin.

6angaren baquwar kuwa waya take tana dube dube kamar marar gaskiya tace" kinga Halima kamar ba abinci taxo nema ba fa bcs ta shiga daga ciki tace na jira ta ta fito mu tafi..... haba sau nawa zan gaya miki abinci taxo nema ina biye da ita a gurin bikin duk abinda take ina sane kawai kije cikin fridge ki sami fresh milk bcs ita ce favourite d'in ta sea ki zuba wannan garin maganin a ciki in yaso ki kama jiki ki bar gidan kafin su fito su riskeki nidai fatana Allah yasa seema ce zata bata fresh milk d'in da hannun ta bcs aikin zai fi kyau but ina kule tun can take nema mata abinda zata ci nasan baza a sami matsala ba ita zata nema mata ko wannan karon ,,,, to gashi kuwa Hajiya seema tayi zaman ta fa a mota bata fito ba har yanzu sae waya take "eh kiyi aikin ki kawai kuma idan ma fresh milk d'in suna da yawa kibi kowace ki saka......Duka fa? .... Eh man to wa yasan wacce zata d'auka a ciki kuma maganin ba kisa yake ba kawai za'a sha wahala wanda in Billy tasha  ko second d'aya yaron cikin ta ba zai qara ba zai mutu,
to kamar yanda yaron cikin ya mutu ba zai sake dawowa ba har abada haka auren seema zai mutu har abada kuma ba zata sake yin aure ba,,,
amma meyasa kike son sae Billy za'a bawa maganin?sbd ita kad'ai na sani mace mai ciki na wata shida bcs boka yace sae cikin wata shida ne zai yi aikin, just kawai kiyi sauri kimin aikina kizo na biyaki ladar ki.
 " ok to"
 Nan  ta tashi ta nufi fridge koda ta bud'e fresh milk kwali d'aya ta samu,
cikin hanzari ta zuba garin maganin ta rufe tana rufe fridge sae ga Hajiya seema ta shigo wanda yayi dai dai da saukowar pinky sae kukan shagwa6a take tana fad'in wai ni ina zan sami fresh milk a gidan nan"
ganin baquwa a gun fridge yasa Hajiya seema tace "yadai wani abu kike so? Eh wai ruwa ne na sha.... Billy da ta qaraso tace" Mtsw yi haquri ban baki ruwa ba na tafi but dan Allah a cikin fridge d'in ko akwai fresh milk ? Eh inaga kamar na ganta a ciki..... Hajiya seema tace" lallai bari muga kamar na hango ta kafin ta rufe fridge d'in,
nan ta bud'e ta d'aukowa Billy wacce ta buga ihun murna ta kar6i fresh milk a hannun Hajiya seema, baquwar tace "Pinky ni zan tafi bcs na kira feenah tayi min misalin gurin ina so naje kafin bikin yayi nisa, ok shikenan sae mun had'u.      
 Daga haka ta fita inda ta manta wayar ta kan seater ba tare da kowa ya lura ba har ta wuce.

Billy kuwa ta bud'e fresh milk zata kafa kwalin gabad'aya a bakin ta sae aka kar6e kwalin tare da cewa "ban fara ra'ayin d'an qaramin bakin nan ya qara girma ba ina cup da baza kisha da shi ba? cikin 6acin rai irin na shagwa6a ta kalli Hakeem wanda ya kar6e kwalin tace "meye haka Bobby ?
ai ke zan cewa meye haka kin baro gurin biki bayan kinsan ba irin bikin da zaki bar guri bane,, ai yanzu komawa zanyi bani fresh milk nasha tukun sae muje dama mama tace ita baza ta koma ba....no ajiye zancen fresh milk kizo muje sauri nake,kuka ta ajiye mai tace "nidai pls ka barni nasha tukun ....idan mun dawo ba,, ya fadi haka ne yayinda umma ta sauko, Billy ta kalli umma cikin kuka tace" umma wai ba zai bari na sha ba har sae mun dawo kuma yunwa nake ji kamar na mutu"

 Hava Hakeem ya tana jin yunwa zaka ce sae kun dawo bayan yunwar ce ta maida ta gida....amma umma shine zata ajiye min kuka bata min bayani ba bayan tasan bana son kukan nan da takeyi kuma yunwa sae kace ba abinci a can duk ina kalolin abincin da kika baro? Bobby bana ra'ayin ko d'aya a cikin su kuma ba fresh milk a gurin....Mtsw ya buga guntun tsaki yaja hannun ta yace"zo muje kya sha ta a cikin mota, qunquni ta shiga yi ita baza ma ta sha ba ko yunwa zata kashe ta kuwa, Hakeem yaji sak me take fad'a yayi shiru kamar bai ji ta ba.
 Da suka shiga mota ya bata fresh milk taqi kar6a nan ya ajiye mata ita kan jikin ta yaja motar cikin 6acin rai.
   Suna isa ta fita tun mota bata qarasa tsayi ba ta kuma jefar da fresh milk kan seat ta wuce kallon ta kawai Hakeem yayi shima ya fito motar ba tare da ya d'auko mata fresh milk in ba.


Tun six sae guraren qarfe tara na dare suka dawo inda har yanzu fishi Billy keyi.
   Sun d'an jima da dawowa ne Hakeem yaje d'akin  Billy ya samu har tayi wanka tana shirin kwanciya zama yayi kusa da ita yana rarrashin ta har ya samu ta haqura suka je d'akin shi.
  Suna shiga d'aki ya bud'e fridge ya d'auko fresh milk da cup yaje ya zauna kusa da ita ya tsiyaya mata a cup yace "ungo kisha tunda muka shigo na sanya miki ita a fridge shine har ta d'an soma yin sanyi,
ba musu ta kar6a takai kan lips kenan taji bata yi sanyi a yanda take so ba cikin fushi ta ajiye cup tace" tun d'azu da ace ka barni nasha da zan fi jin dad'in ta amma sae da ta rage sanyi zaka wani ce nasha,
Tissue ya zaro ya goge mata lips in ta dake dauke da d'igon fresh milk yace "yi haquri bari na sanya miki qanqara tayi sanyi sae kisha kinji" ba ta ce komai ba sae kwanciya tayi kan gadon tana kuka mai cike da shagwa6a,,
Nan Hakeem yaje ya fashe qanqara ya saka mata sae da ya kwatan ci tayi sanyi yace " kukan ya isa haka tashi kisha yanzu tayi dai dai yanda kike so kinji "
nan ta tashi da mazarin ta sbd yunwa take ji sosai,
babyn cikin ta duk ya hana ta saqat sae motsi yake,
"jawota yayi jikin shi zai fara bata yace" bari dai nasha tukun naji idan tayi sanyi yanda kike so kar kiji ba dai dai ba ki ajiye min wani sabon kuka,
nan ya kai cup a bakin sa ya kur6a yace "wow tayi sanyi yanda kike so" oya bud'e bakin ki kisha " nan ta bud'e bakin ta bai riga ya bata ba wani irin tari yazo mishi ba shiri ya ajiye cup ya fara tari har da su zamewa kan gado duk Billy ta rikice ta durqusa kusa da shi tana murza mishi bayan shi sae sannu take mishi.
Ganin tana qoqarin mishi kuka ya samu da qyar ya tsaida tarin yace " is ok ta d'an sarqe ni ne kar kiyi kuka kinji, ungo sha kar yunwa ta miki yawa but take care kema kar ta sarqe ki kinji, gyada mishi kai tayi ya tashi ya nufi toilet cikin sauri sbd tarin da ke qoqarin sake zo mishi,
da shigar shi ya kunna famfo don kar taji sautin tarin da yake wanda kan tsananin wahala har wani kalar amai ya fara yi mara kyan gani.
  Billy kuwa sae da ta qara qanqara tayi zaune tare da kai cup a bakin ta.

*Billy giro 😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 8:42 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [14/9/2016]

*👛BILLY PINKY DURLING 👛*





*Na Billy giro 😊*


*page*
    *👛81&82👛*
Kan tasha ta ajiye cup  ba shiri kan wani news da take kallo a BBC , ta tashi cikin sauri tana fad'in "Bobby zo kaga wani abu da yake faruwa a qasar.....cak komai nata ya tsaya sbd Hakeem da ta samu cikin wani hali zaune da6as duk ya galaibata sae kwara amai yake wanda duk a tunanin ta yazo kuskure bakin sa ne sae ta sami sa6anin haka.
 

  Cike da son tayi kuka ta durqusa kusa da shi sae tambayoyi take mishi, komai Hakeem kasa ce mata yayi sae qoqarin kwanciya yake kan qirjin ta haka ta rungume shi bata damu da aman da ke jikin sa ba duk tabi ta rikice ganin tarin sae abinda ya qaru,duk dibara ta 6ace mata sae kuke ta ajiye tana fad'in "na shiga uku Bobby dan Allah ka daina tarin nan haka"
     Da qyar ya samu yace "stop crying kira min Amjad a waya"
  Nan ta tashi cikin sauri ta nemo waya ta kira Amjad sannan ta koma toilet, ganin tarin ya rage mishi ta d'an ji qarfin cire mishi kayan jikin shi tasa ruwa ta wanke mishi jikin shi inda da qyar ta iya tayadda shi tsaye ta daura mishi towel suka fito.
  Ya kwanta kan bed taje ta debo ruwa a cup ta hau gadon tayi zaune kamar zaman tafiya ta talloboshi tana bashi ruwa da ya gama sha ta kwantar da shi wanda yayi dai dai da jin knocking,
a hankali ta tashi ta nemi hijab ta saka sannan ta bud'e d'aki Amjad ne ya shigo da sallamar shi ta amsa sallamar a sanyaye kafin take fita ta basu guri sae da ya gama bincikar Hakeem ya buqaci ta zo inda ya tambaye ta mene last abinda yaci?tace " fresh milk ce yasha ta sarqe shi shine fa har da su amai,,,no wannan ba zancen sarqewa bane a kawai ko mene but muga fresh milk idan ba expire tayi ba nan ya duba expiring date yaga bata yi expire ba yace" kafin ita me yasha? gaskiya bana iya tuna yaci wani abu bcs ko a gurin biki ba wani abu da nake ganin yaci,,,
  OK to zan mishi allura yanzu zan kuma je da fresh milk by tomorrow na dawo da result d'in binciken da nayi akai, nan ya d'auki ta cup ya zuba a cikin ta kwalin sannan yayi wa Hakeem allura ya fita kafin Billy ke mishi godiya,
bata hau gadon ba sae da ta had'a mishi coffee ta shiga bashi a hankali har yace ya isa haka ajiye cup tayi yayinda take mishi kallon tausayi har dai yanda taga idanun shi sunyi jajir duk jijiyoyin kanshi sun tashi ga jikin shi da yayi zafi sosai sae numfashi yake fitarwa a wahale.
cikin ta yake kallo long time ya kai hannun sa a hankali ya shafi cikin yace"Billyta babyn mu yana motsi da yawa dan Allah je kici wani abu kar ki ce zaki kwanta haka ki haqura kisha quarker oats in yaso da safe a siyo fresh milk kinji " ok Bobby" nan ta tashi taje ta had'o quarker oats tayi zaune tana sha bayan ta gama Hakeem yace ta d'auko kankana su sha wanda yayi haka ne don ta kawai sbd yasan tana son shan kankana kafin su kwanta.
Nan ta dauko plate d'in kankana wacce tayi sanyi, inda ta shiga sha tana bashi yana sha har suka kammala suka kurkure bakin su suka shiga bacci.
 
Da safe cikin juriya yake yin komai har ya samu yayi sallah sae dai ba masallaci yaje ba sbd baya jin qarfin tafiya, bayan sun gama sallah Billy ta kalle shi da kulawa tana mishi sannu cikin sakin fuska yake amsa mata.
   Hijabin jikin ta ta cire ta kwantar da kanshi kan cinyoyin ta inda ta shiga shafar sumar kanshi a hankali daga haka har yayi bacci, sae da baccin sa yayi nisa ta d'auko pillow ta kwantar da kanshi akai ita kuma ta tashi ta shiga gyaran d'akin har zuwa nata d'aki bayan ta fito ta had'a breakfast inda ta sami Baraka na share gidan.

Sae guraren goma ta kammala komai, taje da shirin wankan ta d'akin Hakeem ta samu ya tashi daga bacci sae tari yake cike da ban tausayi har da su aman jini da ya tashi hankalin pinky sosai cikin kuka ta kira umma ta sanar da ita.

Umma ce ta fara zowa kafin Amjad sae da umma ta nemi taji yanda ciwon ya fara, Billy ta gaya mata abinda ta sani daga shan fresh milk nan Amjad yace " gashi kuwa a iya bincike na ban ga wani abu a cikin fresh milk ba wanda za'a ce ko shine yake sa shi tari haka but muje asibiti domin nayi qwaqqwaran bincike akan Hakeem ko za'a gano ainihin ciwon da ke damun shi.

  Sae da Billy da Hakeem sukayi wanka sannan suka kama hanyar asibiti.

Cikin mota Billy sae kuka take yayinda take riqe da handkerchief tana faman sharewa Hakeem jinin da ke fito mishi inda duk yayi tari, duk tabi ta rikice tana ganin kamar Hakeem mutuwa zai yi, umma sae rarrashin ta take wacce ko ita hankalin ta a  tashe yake amma haka ta dake tana nunawa Billy tayi haquri ba wata matsala ba ce.

Bayan sunje asibiti anyi duk iya binciken da za'ayi amma ba a gano komai ba haka suka dawo gida jiki sanyaye inda umma bata shigo gida ba ta tafi domin samowa Hakeem maganin hausa ko Allah zai sa a dace.

Billy kuwa 6angaren su sukaje inda take rungume da Hakeem sae kuka take,
Baraka ce taxo ta same su riqe da waya a hannun ta ta miqawa Billy tare da fad'in  "d'azu naje yiwa umma ina kwana ne ta bani wayar tace na kawo miki wata qil ko baquwar jiya ce ta manta da ita.......
ba shiri pinky ta jefar da wayar ganin yanda Hakeem ya zame jiki sae aman jini yake kwarawa sare sare tace" na shiga uku don Allah Baraka taimaka min da ruwa! A gurguje Baraka taje ta debo ruwa Billy ta kar6i ruwan ta bawa Hakeem ya dakatar da ita yana fad'in "pls pinky ki min add'ua tukun ko Allah zai rage min wannan azabar ba musu ta tofe ruwan da Add'ua ta bashi yasha,
bai fi minti biyar da shan ruwan ba,
tarin ya fara masa sauqi nan Billy ta kama shi suka haura sama domin bawa Baraka gurin ta gyara.
  Suna shiga d'aki ta cire mishi rigar jikin shi ta bar shi da singlet da dogon wando sannan ta nufi downstairs ta debo musu break fast tayi zaune kusa da shi ta fara ciyadda shi yayinda yake kar6a yana ci wanda da qyar yake samu abincin na wuce mishi sbd wani irin ciwo da maqogaron sa ke mishi gashi ba yanda ya iya sbd yunwa yake ji sosai.

Tana kammala bashi abincin ya nemi guri ya kwanta ita kuma ta fara yin nata break fast tana gamawa Hakeem ya nemi ta cire mishi vest in jikin shi sbd zafi yake ji,
nan ta cire mishi hade da qara qarfin Ac,nan ya yunqurawa  zai tashi zaune cikin hanzari Billy ta taimaka mishi,
sae dai tunda ya zauna yaji zaman yana qoqarin gagarar shi duk da jinginawar da yayi a jikin gado, hakan yasa ya kwantar da kanshi kan kafad'ar Billy tare da sakad'o hannun shi ta bayan qugun ta yayinda yakai d'ayan hannun shi ya yaye rigar jikin ta ya fara shafa cikin ta a hankali  inda babyn ya shiga motsi cike da natsuwa Billy sae kallon shi take duk gefen da babyn ya motsa sae Hakeem ya kai hannun sa a gun wanda dama haka yake mata idan suna zaune basa yin komai wai shi a cewar wasa yake ma babyn shi.
    Murmushi ne ya bayyana a fuskar ta kafin take share hawaye ta kalli Hakeem da ya d'ago yana kallon ta tace " my soldier man kaji sauqi ne da naga kana wasa da babyn ka ?  murmushi kawai yayi domin shi kad'ai yasan abinda yake ji,
bai ce mata komai ba sae qirjin ta da yake kallo wanda ya qara cika da tsayi wanda da alama bai lura ba sae yanzu hakan yasa  yakai hannun shi ya bud'e buttons d'in rigar ta yana qarewa qirjin  kallo, kamar mai tsoron ta6awa ya kai hannu yana shafa saman mamman had'e da mamaki a fuskar shi yace"Billyta meyasa qirjin ki ya qara cika haka? da murmushi ta riqo hannun shi ta d'ora kan cikin ta tace"Babyn mu ne ya kawo hakan.

*Billy giro 😊*
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 8:43 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [ 9/15/2016]

*👛BILLY PINKY DURLING 👛*







*Na Billy giro 😊*



*page*

     *👛83&84👛*
Ya akayi kika san hakan? umma na tambaya meyasa qirjin na keta cikowa haka ko qiba ce, tace min cikin da nake d'auke da shine, but Bobby yanzu kana nufin baka ta6a fahimtar cewa qirjina ya ciko  ba sae yau? Ni ma abinda ya d'aure min kai kenan da ban fahimta ba sae a yau,,, well ba mamaki sbd yawan tafiye tafiye bai barka ba, haka ne kuma.
    Daga haka sukayi shiru Hakeem ya katse shirun da cewa "pls Billyta d'an samar min sweet na sa a baki na bcs bana jin dad'in bakin nawa, kamar nawa za'a d'auko? qwara d'aya kawai,
Nan ta tashi ta d'auko mishi ta yaye ledar sweet d'in ta saka mishi a baki.
 sha yake yayinda yake kwance kan cinyoyin ta qamshin sweet sae bugun hancin ta yake,
 a shagwa6e ta kalle shi tace "Bobby en min sweet d'inka,, je ki d'auko mana, maqale kafad'a tayi sbd kasalar tashi take ji hakan yasa ta kai bakin ta a hankali kan nashi tana qoqarin saka harshen ta a ciki, cikin hanzari Hakeem ya hana faruwar hakan ta kalle shi da mamaki tace "Bobby lafiya? Am sorry Billyta ta ya zaki had'a baki na da naki bayan bana da lafiya ba a kuma san ainihin abinda ke damuna ba if ciwon yana transferring ta through slaver fa,
ranta ne yayi mugun 6aci ita har akwai wani ciwo da komai muninsa ace zata guji Hakeem,
tace"ka kyauta Bobby u mean nima idan ina d'auke da ciwo zaka guji yin wani abu dani  don kawai kar ka kwashi ciwon, saurin rufe mata baki yayi bcs ji yayi kamar tayi sa6o yace"pinky shin har kina tunanin akwai wani abu a duniyar nan da zai sa na guje miki..... Eh mana gashi ka nuna min, tayi maganar ne yayinda ta kai hannu kan fuskar ta izuwa kuka, cikin rarrashi Hakeem ya riqo hannun yace "I dn mean to hurt u pls kar kiyi kuka dan Allah" Billy kam sae da ta zubo en hawayen ta sbd sunzo gab,
  Yace "Billyta pls kar ki min asarar wasu hawaye ya isa haka kinji, gyd'a mishi kai tayi yace" yauwa to zo na share miki hawayen, ba musu ta fad'a kan qirjin shi ta wani lafe kamar wacce zata sha mamma shi kuma ya shiga share mata hawaye yana fad'in "I'm really sorry banyi haka ba sae don gudun kar ke da Babyn mu ku sami ciwon mu zo mu duka uku ba lafiya, bugo qirjin sa tayi a shagwa6e tace" nifa ka daina zancen nan kawai ka ba ni sweet d'in nasha koma mene ne mu d'auka d'in ba komai, ba musu ya ciro sweet d'in bakin sa ya saka mata murmushi tayi tare da d'ora mishi kiss tace"yi haquri bari na d'auko maka wani, girgiza kanshi yayi yace"Billyta kenan wai dama ba qiwuyar tashi kike ji bane? Eh but wa kaina nake ji ma qiwuya amma in don kaine ba komai ko misira ne zanje"
ta fad'i haka ne yayinda ta d'auko sweet ta 6are leda ta saka mishi a baki wanda yayi dai dai da jin knocking, zuwa tayi ta bud'e qofa ta sami Baraka a tsaye, Baraka tace "gashi wayar nan da kika jefar tun d'azu sae faman kira ake" Billy ta kar6i waya ta rufe qofa kan tayi receiving wayar ta tsinke taje ta zauna Hakeem ya kar6i wayar yana dubawa yace "wayar waye? wai wata qawar feenah ce taxo jiya tana so zata je event d'in da ake yi shine ta manta wayar,, ok yauwa ungo an sake kira,
nan Billy ta kar6i wayar inda taga Anti Halima na yawo kan sikirin d'aga wayar tayi kafin tace komai" Halima ta fara cewa amma ke ba er iska irin ki kin san baza ki iya aikin ba shine kika sa na baki,
gashi kinsan boka yace a wannan ranar ake so Billy tasha wannan magani idan ranar ta wuce ko tasha yaron cikin ta ba zai mutu ba domint maganin ba zai yi aiki ba bare har buri na ya cika na ganin na lalata auren seema gashi kin shantaqe tun jiya ba ke ba labarin ki bare naji bayani, kuma sae faman kiran ki nake ba kya d'aga waya lafiya me yake faruwa ne!ina ce dai kinyi nasarar saka wannan garin maganin a fresh milk?
mtsw ya kimin shiru kimin magana mana!
   Billy kam saurin rufe bakin ta tayi sbd kukan da ke qoqarin kufce mata sae kallon cikin ta take kafin take kallon Hakeem da ke qoqarin yi mata magana Yace"Billyta... Saurin rufe mai baki tayi ta d'ora mishi wayar a kunne, inda Halima sae fad'a take tana cewa "ke ni kimin magana nasan sak kina ji na gara ma ki daina wani pretending so nake kawai naji idan kin kasa aikin ki gaya min yau na koma gurin boka na sami wata mafitar kar lokaci ya qure min!..... nan Hakeem ya kashe wayar ya kalli Billy wacce ta fara fitar da sautin kuka,
 ya rungume ta ya na lallashi yace "bangane me yake faruwa ba but kamar nasan voice d'in matar nan wace ce ita?
cikin kuka tace" Anti Halima ce qawar mama wai......ta qarasa gaya mishi duk abinda taji a waya inda hankalin Hakeem ya tashi sosai ya shiga tambayar ta idan jiya bata sha fresh milk d'in ba bayan tafiyar sa toilet tace"um um ban sha ba"ajiyar zuciya ya sauke yayinda wayar baquwa ta shiga ruri, rai 6ace ya d'auki wayar har yana niyar cika ta da masifa sae kuma ya fasa ya canza amon muryar shi tare da "fad'in kiyi haquri mai wayar bacci take ta d'aga wayar ne a bisa rashin  sani
 but me za a ce mata idan ta farka..... kai waye? ni boy friend d'in ta ne.... Mtsw kaji matsalar wato baqar jarabar ta ce ta motsa shine har ta kasa zowa ta min bayani to idan ta farka ka gaya mata ta same ni a gida not family house gida na da nake zama ni kad'ai, to shike nan yanzun nan zan tashe  ta kuwa na sanar da ita.....da yafi domin idan naga ta jima zan iya zuwa na same ku koma a wane hotel ne!
nan ta katse wayar ya kalli Billy yace " hurry up! shirya muje wlh yau kashin ta ya bushe sae naga bayan ta kafin maganin nan ya qarasa illata ni, Billy kam duk ta rud'e ta kasa yin komai sae Hakeem ne ya shirya ta ya dauki bindiga suka kama hanyar zuwa gidan Halima inda suka kira umma da Hajiya seema da kuma Abban Billy da na Hakeem a cewar su same su a can akwai magana.

 Ba qaramin tashin hankali Halima ta shiga  ba da jin abinda ya kawo su hakeem amma haka ta dake kan cewa ba ita ce yayi waya da ita ba yaje can ya nemi koma wace ce kar ya tayar mata hayaniya a gida, cikin tsananin 6acin rai  Hakeem ya d'ora mata bindiga a goshi yace sae tayi bayanin abinda take shirin aiwatar wa ko kuma ya harbe ta yanzu! ai kuwa nan jikin ta ya d'auki rawa duk ta rud'e tana mishi bayani bayan ta gama yace "Alhmdlh Allah ya kare Billyta domin ni nasha maganin ba ita ba don haka kafin na mutu sae na kashe ki tukun.......don Allah kar ka kashe ni wlh ba maganin mutuwa bane yaron ciki kawai yake kashewa kuma banyi hakan ba sae don na raba auren seema amma don Allah kuyi haquri nan ta shiga basu haquri har tana qoqarin kama qafafun Billy ,
Nan Hakeem ya shiga shuri da ita yana "fad'in wa zaki roqa gafara da kike tunanin zai yafe miki"
Haka ya bita sae buga mata kan bindiga yake  a ka inda nan take kan ta ya fashe sae jini yake fitarwa,bai damu da ganin jinin ba sae dukan ta yake ci gaba da yi domin har ga Allah kashe ta yake da niyar yi sbd zuciya ta riga ta kawo masa iya wuya.
Billy sai kallon ikon Allah take domin bata ta6a ganin Hakeem ya hasala irin yau ba duk tabi ta tsorace tana gudun kar yayi kisa hakan yasa taje ta riqe bindigar inda a zuciye Hakeem ya kar6e bindigar wanda by mistake ya harba bindigar ta sami ginar d'akin, yayinda Billy ta saki wani irin razanannen ihu ta  qanqame Hakeem kamar wacce zata shige cikin jikin shi sae kuka take a tsorace duk jikin ta ya d'auki rawa gabad'aya.

Su Abba ne suka shigo suna tambayar lafiya me yake faruwa haka da har muke jin qarar bindiga kafin mu shigo? Wani mugun kallo Hakeem ya yi wa Halima yace "ai sae ki musu bayanin muguntar da kika tashi aiwatarwa la'ananniyar mata kawai!
ba musu ta shiga yi musu bayanin komai har tana roqon su gafara inda gabad'ayan su suka yi tir da abinda suka ji, yayinda Hakeem yake ta faman rarrashin Billy ,a  kafaice yakai  hannu kan cikin ta sbd wani  irin juyi da  yaji babyn nayi nan yaji baya da wata natsuwa sae sunje asibiti sbd motsin ya wuce yanda Babyn ke motsawa ko yaushe hakan yasa ya kira police  a gaggauce  suka zo suka tafi da Halima domin a bata azabar da ko kare baza qara tunanin illatawa ba.

Gabad'ayan su suka dunguma zuwa asibiti
aka duba ta ba wata matsala inda Amjad ya sanar da su razanace kawai,,,
Nan suka kama hanyar komawa gida cike da tu'ajjabi da kuma jin dadin nasarar Billy bata sha fresh milk d'in ba.

Har suka isa gida  jikin Billy qyarma yake.

Fitowa sukayi cikin mota yayinda Hakeem yake riqe da hannun Billy,
 ya d'auko bindiga zai shiga da ita cikin gida ,
 Billy tayi saurin shigewa jikin shi kan bata son bindigar ta ta6a ta  hakan yasa ko moving Hakeem ya kasa yi sbd yanda ta shige jikin shi yace"is ok Billyta bindigar baza ta ta6a ki ba kinga na ma mayarda ita a cikin mota " nan ya samu ta sassauta riqon da ta mishi suka shiga cikin gida.

Suna isa gida Hakeem ya shiga toilet domin watsa ruwa wanda kafin yaje sae da ya tambayi Billy ko tana buqatar watsa ruwa tace mishi a'a.
  Bai wani  jima ba ya fito ya sami Billy inda ya barta sae kallon shi take d'ari d'ari kamar wata mai jin  shakkun shi  ,
jiki sanyaye ta tashi zata bar dakin Hakeem da ke neman tufafin sawa ya bita da ido kafin yake cewa" Billyta ina zuwa? zanje d'aki "tayi maganar ne cikin yanayi na son yin kuka, a hankali ya qaraso gurin ta tare da d'ago fuskar ta yana kallon idanun ta da suka ciko.
  Nan ta fad'a kan jikin shi tana kuka cikin shagwa6a,
 Hakeem ya shiga bubbuga bayan ta alamar rarrashi yace"Billyta mene ne?uhm uhm Bobby meyasa ka harba bindiga kasa na tsorata da yawa yanzu gashi kaina sae ciwo yake ta min,,, am very sorry its by mistake amma kuma shine da muka je asibiti baki fad'i cewa kanki na miki ciwo ba,,, ni bana so magungunan da Amjad keta rubuta mana ,,ni kuma banaso kina fama da ciwo ki zauna ba shan magani don haka ko yanzu baki tsira ba ,tashi tayi tana qoqarin barin d'akin yace"kar ki fita fa,,,Bobby dan Allah kayi haquri na fita,, idan kin sha magani ba, dar6ashewa tayi gurin ta jingina a jikin qofa ta had'e kai da guiwa tana rera kuka kamar  wata marainiya  ,sae da ya d'auko magani da ruwa  yazo ya durqusa kusa da ita yace"da kisha magani da a miki allura wanne kike so?ko d'aya ,,,yi haquri dai ki za6i d'aya.... Allah ko d'aya bana so,kinga fa am not in mood just ina lalla6a ki ne don haka kar ki kaini maqura domin lafiyar ki ta fimin komai,oya kar6i kisha, jiki sanyaye ta bud'e baki ya saka mata magani sannan yakai cup d'in ruwa a bakin ta,ta had'iye maganin yayinda hawaye ke qoqarin zubowa a idon ta ta kalli Hakeem sau d'aya ta kauda kai ta tashi ta tafi d'akin ta tayi kwance kan bed tana kuka marar sauti ,Hakeem da ya biyo ta ya zauna kusa da ita yace "wai Billy meyasa kika maida kuka ba komai ba bayan kinsan a gurina azaba ce  amma ko wace safiya sai kinyi kuka hankalin ki ke kwanciya,
 shin ko wani  laifi na miki da kike azabtar dani kullum ko kuma so na ne ba kya yi shiyasa baki damu da azabar da nake ji ba.

 Tashi tayi tare da kama kunnen tace"pls Bobby kayi haquri nima haka nake samun kaina da kuka komai qanqantar abu amma wlh ina sonka kukan da nakeyi bada niya bane ya riga ya zamo min jiki ban kuma san ta yanda zan fara dainawa ba but i will try my best naga cewa na daina kuka any how kaji,,, naji Billyta ,ya fad'i haka ne yayinda ya Kwantar da kanta kan qirjin shi sukayi shiru ba mai cewa komai sae Billy da ke shafar qirjin Hakeem a hankali .
sannu sannu take jin bacci har baccin ya d'auke ta.
  Kwantar da ita kan bed yayi domin yana son ya fita sbd case d'in Halima wanda yake so ya gano wace ce ta turo har tasa garin magani a fresh milk.

Tun bayan zuhur da ya fita bai dawo ba sae bayan sallar la'asar ma'ana sae da yayi bincike shida police har suka gano wannan yarinyar wacce tun jiya da ta saka garin magani ta fita tayi had'arin mota shine aka kaita asibiti inda yanzu Hakeem yasa an kaita cell a cewar tayi jinya a can in taqamar ta mugunta. wanda kafin ya baro gurin su ba irin roqon da basu mishi ba kan yayi haquri yasa a fitar da su sun tuba baza su sake ba amma tamkar bada Hakeem suke zancen ba yayi tafiyar sa.

6angaren su umma ya fara zuwa ya sanar da su yanda ya kwashe da su Halima ya kuma ce bazai sa a fitar da su ba sae sunsha azaba mai tsanani.

 umma da Hajiya seema suka ce hakan yayi dai dai ai gobe baza su qara tunanin yiwa wani  ba,
nan yayi sallama da su ya tafi 6angaren su ya samu Billy ta gama sallah tayi kwance  a gurin da tayi sallah sae yawo take da d'an yatsan ta tana bin zanen  masallacin da ke kan  carpet.

 Sallamar da taji ne yasa ta d'agowa taje a hankali ta rungumo shi tana mishi sannu da zuwa tare da kar6ar ledar da ke hannun shi.

Kan carpet din sallah suka je suka zauna Hakeem ya buqaci Billy da ta ware  musu leda.
  fresh milk ce da gasasshiyar kaza sae ice cream nan ta tashi ta d'auko musu plate suka ci sae da suka qoshi  ,Hakeem yace"Billyta ko zaki iya hallatar event d'in da za'ayi anjima ko kuma naje ni kadai? Eh zan iya zuwa, goshin ta ya shafo tare da fad'in"kan naki ya daina ciwo ne?eh koda na tashi daga bacci ya daina min ciwo, thank God yanzu saka mana ice cream d'in nan a fridge tunda yanzu ba mu da lokacin shan shi.
 Bayan ta saka yace"muje muyi wanka mu shirya.

A nan d'akin sukayi wanka da suka shirya suka fita inda cikin mota Hakeem ke sanar da ita cewa sun nemo wannan baquwar ashe qarya take ba qawar Feenah ba ce kuma tana fita tayi accident  shine bata sami isa gun Halima ba.

Nan Billy ta maida hankali tana sauraren shi da qarshe tace"Allah ya shirye su mu kuma Allah ya qara kare mu da kariyar sa .
  Hakeem yace"Amin" wanda yayi dai da sun iso.

Billy na zuwa ta sami Feenah sae fushi take da ita nan ta sanar da ita abinda ke faruwa ai kuwa ta shiga tsinewa su Halima.


Sae dare suka dawo yayinda suka shigo da kayayyakin da Hakeem ya siyo da za a buqata kamar su fresh milk da sauran su .

A gajiye suka fad'a wanka sukayi zaune suna hutawa yayinda suke shan ice cream.


Washe gari ne aka d'aura auren feenah da naini inda kowa yayi farin ciki da d'aurin auren  .


Da yamma akayi wankin amarya to ten aka kaita.


Zuwa 11:30pm su Billy sun dawo gida har sunyi wanka inda Hakeem sae tsula wa Billy tsiya yake wai shima yau fa ango ne yana buqatar amaryar  shi.

 Duk da a gajiye take amma bata nuna mishi ba sbd tasan Hakeem mutum ne mai haquri da ya kan iya jimawa bai buqaci haqqin sa ba.

 Nan ta ba da kai bori ya hau  suka faranta ran junan su sosai sbd sun jima basu zagayi duniyar ma'aurata ba.



A kwana a tashi ba wuya a gurin Allah inda yau cikin Billy ya cika wata tara shagwa6a kuma sae abinda ya qaru a gun Billy domin tunda cikin ta ya fara mata nauyi   komai Hakeem ke mata.


kukan shagwa6a take yiwa Hakeem har da su buga qafa a qasa duk da tulun cikin da ke gaban ta kuwa wanda tana yin shagwa6ar ne kan cewa ita idan ta haifu a 6angaren su umma zata koma da zama Hakeem kuma yace ba a yi haka ba sae dai gwaggo ta dawo 6angaren su da zama .hakan yasa ta kuka tana magana cikin shagwa6a shi kuma yana maida mata amsa cikin irin yanda take magana kamar haka:
 "Uhm uhm don Allah dai Bobby kayi haquri ni naje ba sae gwaggo tazo ba"......"um um dan Allah dai ke kiyi haquri gwaggo tazo"......"Dan Allah dai ku amsa mana sallamar da muke tayi tun d'azu"

 Naini ne
 yayi maganar irin yanda yaji suna yi  wanda yazo ne shida Feenah wacce ke d'auke da qaramin cikin ta na wata biyu.

Dariya sukayi gabad'aya har Billy da ke d'auke da hawaye kan kumatun ta.


A nan suka yini sae dare suka tafi.



zaune suke kan gado yayinda Billy ke sanye da half vest da guntun wando tana  zaune a tsakkiyar  qafafun Hakeem,
 shi kuma yana rungume da ita ta baya ya sakad'o hannayen sa kan tulun cikin ta yana wasa da Babyn shi ,
Billy sae murmushi take tana kallon wasar,
   ta shafo gefen fuskar Hakeem tace"Bobby wasan ya isa haka ina son nayi bacci"Billyta wasan yana min dad'i har dai yanda naga yau babyn sae motsi yake tayi,,
Ok ni kan ma kwanciya zanyi idan ka gama wasan sea ka rufa min blanket....Aa tunda bacci zakiyi na daina wasan ni ma zan bi sahun ki.


Nan suka kwanta tare da kashe wutar d'akin.




Cikin bacci Hakeem yake jin ihun Billy kamar a mafarki sae kiran sunan shi take ya tashi firgigit ya nufi toilet inda yake jin sautin kukan ta.

Koda ya shiga ya samu duk tayi zufa zufa sae kuka take tana yarfi da hannu,
 da hanzarin shi ya kwa6e rigar jikin shi ya durqusa yana share mata gumi duk ya rud'e yana tambayar meye yake  faruwa?
 cikin kuka mai nuna ta jima tana wahala tace"wayyo Allah Bobby bayana ciwo zan mutu!......ihu ta saki tana fizgar wandon jikin ta ,
a rikice Hakeem ya taya ta cire wandon ,
nan tayi wani irin nishi mai qarfi .


 Fit!qatotuwar jinjira ta fito jawur da ita nan kawai Billy ta jingina a jikin gina tana sauke wahalallen numfashi ,Hakeem kuma jaririyar yake kallo hade da cibiyar da ke reto a jikin Billy uwar tafiya bata riga tafito ba yace"Billyta gaya min yanda zanyi da wannan abun da ke reto a tsakanin ku ?
I dnt know Bobby ,
 da qyar ta samu ta furta hakan sae kawai ta sulale ta some mishi a gurin,
 a rikice ya shiga kiran sunan ta yana jijjiga ta amma bata motsa ba ga jinjira sae tsala ihu take nan ya tafi a gurguje yaje 6angaren su umma ya kira ta tana zowa ta samu uwar tafiya ta fad'o sannan suka kwasa sukayi asibiti.

 Ba a sha wata wahala ba ta farfad'o inda ba a sallame su ba sae da aka tabbatar da lafiyar ta ita da baby.


Zaune yake a bayan ta ya d'an kwanto mata kad'an  qafafuwan shi a bud'e suke wanda hakan yasa Billy da ke rungume da baby take zaune a tsakiyar qafafun nashi.

Wani  irin farin ciki ne ke fizgar shi yayinda yake shafa kan jaririyar a hankali wacce sak Billy ce ta kwaso sae duk Hakeem yaji ya qara son Billy .

Kallon ta yake cike da so yace "Billyta a taimakawa babyna da mamma tasha ko"
ba musu ta shiga bud'e buttons d'in rigar ta inda suka kama mamman a tare suka
saka a bakin Baby.



*Billy giro😊*  
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛
[9/22, 8:44 PM] ‪+234 810 038 8117‬: [9/17/2016]


*👛BILLY PINKY DURLING👛*







*Na Billy giro😊*



*page*
    *👛85👛*
Babyn kuwa ta kama tsutsan mamman .
  Yayinda Billy ta d'an maqe jikin ta kad'an ,
  Hakeem yace yadai Billyta da zafi ne?A'a ba wani  zafi sosai kawai dai wani  abu naji yayinda ta kama nipple tana tsutsa,,murmushi yayi yace kinsan shine na farko dole zaki ji wani  abu.
 Nan ya qara d'ago baby domin taji dad'in shan mamman inda ya kai hannu yana qara saka mata mamman a baki, umma ce ta fito daga toilet ta same su tace"oh ni!
wai kai wane irin rashin kunya ne ke damun ka kuma kai da nace kar ka shigo sae na kammala gyara d'akin nan amma shine sae da ka shigo hankalin ka ya kwanta"
yi haquri umma wlh na qagu ne kuma tun dazu su Amjad da Naini suke falo suna son ganin Baby shine nake so tasha mamma tukun......yanzu a cikin daren nan ka taso su... Umma wane dare an fayi asuba yanzun nan ma muka fito daga masallaci... to fita dai ka bamu guri tukun in baby ta gama shan mamma kazo ka kar6e ta.
  Cikin dariya ya tashi har yana had'awa da d'an gudu ya fita sbd yanda umma ke korar shi tana fad'in "kazo kayi zaune a bayan ta kana bawa Baby mamma sae kace kaine mai mamman"

 Billy dai murmushi kawai tayi tana ci gaba da shayadda Baby.


Washe gari en barka sae shigowa suke kamar gidan biki su Feenah da en school dinsu duk ba wanda bai zo ba,Haka ko abokanan Hakeem.


Ranar suna yarinya taci sunan *Sukainat*(that's my lovely sister's Name)
    inda akayi biki shagali tamkar ba a mutuwa.

 Sosai Hakeem ke bawa er shi kulawa ko yaushe yana riqe da ita har yana ji kamar kar a kar6e ta daga hannun shi.


Sannu sannu lokaci keta tafiya yanzu har Sukainat tayi wata uku yarinya tayi kyau tayi wayo ta kuma qara qiba er tu6ul tu6ul jawur da ita kamar ka qwanta jini ya fito son kowa qin wanda ya rasa domin kallo d'aya  zakayi mata kaji ta shiga ranka har dai yanda gashin kanta ya fito liya liya ga sul6i da laushi kamar d'iyar indiyawa.


Hakeem ne kwance  sanye da singlet da dogon wando yayinda Sukainat ke kwance  kan qirjin sa yana shafar sumar kanta a hankali har izuwa gadon bayan ta wanda yana mata haka ne sbd baccin da yake son tayi.

Ba jimawa kuwa baccin ya dauke ta yayinda Billy ta fito daga wanka  tana tsane gashin kanta da d'an qaramin towel .


Hakeem ya tsure fatar jikin ta da kallo wacce ta qara kyau da lafiya.
    Ajiyar zuciya ya sauke sbd tsananin sha'awar ta da yake
ji bcs tun lokacin da ta haifu bai sake neman haqqin sa ba har dai da umma ta masa kwankwami kan kar yaga Billy na gurin shi yace zai nemi haqqin sa ya bari sae jikin ta yayi qwari tukun zuwa  tayi arba'in .
shine har yanzu bai nemi haqqin shi ba a cewar lafiyar Billy ta fi masa komai.

Tashi yayi yaje ya shimfid'e Sukainat kan d'an qaramin gadon ta inda sae da ya mata addu'a kafin yake barin gurin.

 Billy da ke kallon shi ta saki murmushin da ya qara bayyanar da kyaun ta  tare da ware hannyen ta tace"nima a d'auke ni amin addu'a nayi bacci "
  Kamar jira yake yazo da murmushi ya d'auke ta cak suka fad'a kan gado tare da qoqarin zare mata towel d"in jikin ta,turo baki tayi
 tace "Bobby addu'a fa na ce ka min"
A hankali ya lumshe idanun shi tare da d'ora mata kiss kan bakin ta da ta turo yace"ai shirin bacci zan miki tukun ko kuma haka zakiyi bacci da towel?
   "ok to bari na nemo kayan baccin"
  ta fadi haka ne yayinda take yunqurin tashi sae dai Hakeem da yayi mata rumfa yaqi ya d'aga sae faman kallon ta yake cike da sha'awa tace"lafiya Bobby me kake so? wannan nake so,
kunya taji ta d'an kauda fuskar ta kad'an tana murmushi yace"ko baza ki iya bane kar na takura ki?shiru ta mishi yayinda still murmushin jin kunya na kan fuskar ta.

 Yace" pls Billyta say something zaki iya ko na bar ki kiyi bacci? Rufe fuskar ta tayi da tafukan hannayen ta tace mishi "zan iya"
dad'i yaji har cikin ransa har ya saki d'an murmushi yana mai kallon yanayin jin kunyar ta ,
nan ta bude fuskar ta a hankali tana kalloñ dimples dinsa da suka lotsa kan murmushin da yake,
 takai en yatsun ta ta lotsa su a ciki,
 hakeem ya riqo yatsun wanda daga nan ya fara mata abubuwa yayinda take mayar masa da martani har sae da suka jima suna wasa da jikin junan su sannan suka lula duniyar ma'aurata wacce sukayi matuqar jin dad'in ta sosai har ma suna sambatu sae dai sambatun ba komai bane face furta  irin yanda suke matuqar son junan su.



WOW! ALHAMDULILLAH!! NA GODE ALLAH DA YA BANI IKON KAMMALA WANNAN LABARI LAFIYA WANDA NA SAUDAUKAR DA SHI NE GA MY LOVELY LADY (FUTUHATUL-KHAIR)😍

INDA NAYI KUSKURE INA ROQON ALLAH YA YAFE MIN .

  THEN MASOYAN AFRAH KO AMRAH INA FATAR BAKUYI FISHI DA MU BA INSHA'ALLAH BY TOMORROW ZAMU CI GABA DA INDA MUKA TSAYA WATO ZAMU TASHI A 31 PAGE SANNAN KUMA BILLY DA HAKEEM ZASU KASANCE CIKIN AFRAH KO AMRAH DOMIN SU KASANCE MASU TAIMAKAWA AFRAH A BISA HALIN DA ZATA SHIGA CIKI.

LUV U ALL❤

NI BILKEESU ABUBUKAR GIRO KECE MUKU MA'ASSALAM YA MASOYANAH!
👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛👛

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *