Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, September 4, 2017

BA NI NA KASHE TABA

adsense here


→BA NI NA KASHE TABA← PART 1 na bigboy isah
me yasa kakashe ta me tama kane da zaka kashe
musu ita banyi zatan zaka iya kisan kaiba
zaharaddin sannan ta sake shi daga shake mai
wuya da tayi idanun shi sunyi nare nare ta koma
gefe tana kuka a hankali idan shi cike da kwalla ya
durkusa yace momy wllh BANI NA KASHE TABA
cikin kuka ya karashe maganar yace amma nasan
ba wanda zai saurare ni ya fashe da matsanan cin
kuka abun tausayi ji sukayi ana girgiza get din
gidan kamar za'a karya shi Daga ji kasan katti ne
majiya karfi a kofar gidan sai cewa suke wllh a fito
muna da dan mafia nan bazamu yarda ba ya yanka
masoyiyar sa bale yaran mu da kannan mu ay wllh
bazamu yarda ba sai mun kashe shi shima. da
maman deeny da kuma shi kanshi zaharadeen din
duk sun firgita da jin kalaman jama'ar nan na kofar
gida tunani suke ya za'ayi lalai idan ta basu deenyta
kashe shi zasuyi shima tunani yake bazai iya mika
kansa ba idan ya mutu mahaifiyar sa wane hali zata
shiga. suna ta faman saka wannan kwance wancan
su kuwa matasan nan tuni sun gaji kuma sunga
anki bude get hakan yasa aka nemo jarkar man
fetur a cewar su idan suka ji an fara toya gidan sa
fito su kuma sai su kama zaharadeen din su kashe
kamar yadda suke zargin yayi kisan kai. haka suka
fara watsa fetur a gidan su momy suna cikin tunani
sai sukaji ana jika su da ruwan fetur da dai suka
fahimci fetur ne sai duk suka tsorata jikin su ya
fara bari suka rasa abun yi momy cewa take cikin
kuka ay kaga abunda ka jawo mana yanzu gashi
zasu toya mu da rai kamar wasu yan wuta lol.
deeny yace wllh momy BANI NA NA KASHE TABA
momy tace towa ya kashe ta hawaye kawai naga
ya sake zubowa a fuskar shi karan jiniyar motar
police suka ji a waje ana ta koran mutane da ke
kokarin cin nawa gidan wuta dan har an samo
ashana ana kokarin kyastawa police da duka suka
kori mutane suka je kofar gidan cikin murya me
karfi suka ce zaharadeen ka fito ka mika kanka ga
hukuma dan tabatar da rashin laifin ka ko kuma
laifin jikin shi na rawa sai kuka yake yana wallh
BANI NA KASHE TABA2 momy ta kama hannun shi
tace hakuri zamuyi mu rungumi kaddara isha allah
bazaka cutu ba kayi hakuri ka mika kanka ina ga
hakan zaifi sauki. a gare mu ta karashe maganar ta
cikin kuka haka ya tashi yana tafe yana hawaye
yana juyowa kamar ya bude get din kuma kamar ya
bari a cikin zuciyar shi kuwa yace gwara in fita a
kashe ni ma hakan zaifi min sauki ya kalla sama
yace allah ka fitar dani daga zargin nan da ake min
yana bude get wani police yayi carat ya damke shi
gam sannan wani ta kama hannayan shi ya maida
su baya aka samai ankwa a hannayan shi aka tura
kyyarshi har cikin motar police din mutane ne suka
fara jifar shi suna sai mun kashe ka wllh bazamu
barka ba haka yasa police din cikin hanzari ya
warci motar tasu sai police station ana zuwa aka
nufi sel da shi aka rufe ganin an rufe deeny a sel
yasa na tsaya nan ku biyu ni dan jin labarin

→»ku dinga comment
→»yan mata da samari ayi invite
→»dan momy na gaisuwa
↓Yauwa haka nakeso
comment↓
bigboy



→BANI NA KASHE TA BA← PART 2 na bigboy isa
a gidan su halima kuwa ganin su nayi jigum jigum
kowa yayi ta gumi sai hawaye hajja hauwa hawaye
take tana fadin zaharadeen ashe ba san halima
kake ba ashe duk san da kake na kaje ka kashe ta
ne kayi kudi da ita ta karashe maganar da fashewa
da kuka kacuce mu deeny kaci amanar mu ka
kashe muna yar mu wace ita kadai muka haifa. kiyi
hakuri maman halima wllh wllh wllh sai an kwatar
muna hakin mu sai inda karfina ya kare wllh bazai
kashe muna diya a banza ba sai an kashe shi
shima hawaye ne suka gangaro fuskar shi. jikin
fushi ya tashi ya fita hajja hauwa kuwa kanta a
kasa kuka kawai take. momy kuwa tana ji an tafi da
deenyta cikin hanzari ta dakko hajib dinta ta saka ta
fito da sauri ta kulle gidan kunya duk ta cikata duk
majalisar data wuce ana nunata ana cewa ga
mahaifiyar yaran nan da kashe budurwar sa haka
tata wucewa ana nunata har takai gidan su kawun
deeny wanda shine kanin mahaifin deeny da yake
allah ya amshi ran mijin nata wanda shine mahaifin
zaharadeen tana shiga cikin gidan da sallamar ta
aka amsa ta shiga suka gaisa da amina matar
kawo kenan aka zubo mata koko da kosai dama
bata karya ba amma ko kallan shi batayi ba saboda
abunda ke damun ta su kam basu san komai ke
nan ba saboda labari bai kawo musu nan ba amina
matar kawu tace mamar deeny lafiya naga duk
fuskar ki cike da damuwa daidai nan ne kawu ya
fito daga ban daki kallo daya yama matar yayan
nashi yagane ba lafiya ba alamun tasha kuka ya
karaso wajan a lokacin da yake tambayar ta lafiya
kuwa tana kallan shi ta fashe da kuka a lokacin ne
duk sukayo kanta suna menene ya faru mamar
deeny lafiya kuwa. nan ta fara magana cikin kuka
tana deeny ne da maryam ta maimaita3 har sau
uku cikin kuka ta kasa fada.amina ce ta kamata
tana rarashin ta sannan tadan rage kukan kawu
yace me yasama zaharadeen din da maryam
kuma? nan ta fara shesheka tana musu bayani.tace
maryam tun jiya da ta fita islamiya jiya da yamma
to bata sake dawowa ba har yanzu deeny kuma a
yanzu maganar da nake muku yan sanda sun kama
shi sun tafi da shi wai ana zargin shi da kisan kai
nan ta fashe da kuka su kuma duk suka kama
inalilahhiwa ina ilaihir raji'u
inalilahhiwa ina ilaihir raji'u
inalilahhiwa ina ilaihir raji'u
suke fasa
*****************
acan kuma DPO ne yasa deeny a gaba yana
bazaka fada mana gaskiya ka hutar da kanka kuma
ka hutar damu ba yace yalabai wllh wllh BANI NA
KASHE TA BA dpo ya kara kallan shi yace watto sai
jikin ka yayi tsami zaka fada ko?…… tsoran kar a
hada dani ne yasa na tsaya a nan nima
mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group
bigboy
.


→BANI NA KASHE TABA← PART 3
na bigboy isah
a ranar koni da nake gefe na tausayawa
zaharadeen irin dukan da yasha suna dukan shi
suna bazaka fada mana gaskiya ba shidai abun da
yake cewa kawai wllh BANI NA KASHE TABA. BANI
NA KASHE TABA FA. haka akaci gaba da narkar shi
wai yaki fadan gaskiya har saida ya sume.
***************maman deeny kuwa gidan kawu ta
koma da zama kullum cikin kuka tana tunanin halin
da ta tsinci kanta a ciki yaran ta biyu su duka ba
daya har gwara shi deeny ma tunda ansan yana
hannun yan sanda amma ita kanwar tasa maryam
kenan ba'a san inda take ba kawu yayi yawo har ya
gaji ya dawo gida yana yin sallama suka amsa su
mashi da sauri maman deeny ta mike tana fadin
angan ta anga maryam dina kuwa? gani tayi ya
sunkuyar da kanshi kasa alamun ba labari kenan ai
kuwa ta dora hannun wanta akai ta saka uban kuka
matar kawu dake gefe ita ce ta taso ta rungume ta
tana cewa haba maman deeny hakuri zakiyi kuka
ba namu bane adda'u itace ma fita a wannan lamari
ita ma hawayan ne a fuskar ta. salama suka jiyo a
kofar gida da sauri kawu ya fita dan ganin wake
sallama police yagani cikin kayan aikin sa dan
sandar ya mikawa kawo hannun suka gaisa sannan
dan sandar yace kaine kanin mahaifin zaharadeen
ko kawu yace kwarai kuwa nine police din ya ciro
wata farar takar da ya mikawa kawo yace wannan
san maci ne daga kotu ku gaugauta samun lauya
domin gobe gobe zamu shiga kotu a bisa kes din
danku dan yaki amsa laifin sa a hannun mu kawu
ya karba hannun shi har bari yake yace na gode
sukayi ban kwana har ya juya zai shiga gida dan
sandar yace amma fa ku gaugau ta samun lauyan
ku saboda gobe ko baku da wani lauya bazai hana
zamanan ba a gobe haka kawu ya koma cikin gida
cike da damuwa yana ta tunanin shi ba kudi gare
shi ba ga basu dawa kadara da zasu sayar su
dauka lauya. abban aliyu me ya faru maman deeny
ce ta je4 mai wannan tambaya bai ce mata komai
ba kawai takardar dake hannun sa ya mika mata ta
karba tana bude wa ta fara karantawa sai hawaye
tana tunanin a ina zasu sama lauya Barrister
fadilah ta tuna sai sukaji tace alhmdulilah suka juya
suna kallan ta itama juyowa tayi sannan tace inada
kawata Barrister fadilah nasan tabbas zata taimaka
min idan na nufe ta da wannan alamarin sannan
kwarariyar lauya ce itama. gaba daya sukace
alhamdulilah saiki tashi ki shirya maman aliyu ta
rakaki inji kawu.
mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group
bigboy






on-line 14.04 21:00
→BANI NA KASHE TABA← PART 4
na bigboy isah
******************
alamarin maryam kuwa ranar asabar tayi wankan
ta tasaka kayan islamiya tayi ayr kwaliyar ta ta
dauko jakar qura'a nin ta ta fito tace mama zan tafi
makaranta maman deeny tace to maryam adawo
lafiya ayi karatu da kyau tace to momy zamu dage.
har ta fara tafiya tayi taku uku sai kuma ta juyo
tace momy wai har yanzu su yaya zaharadeen
shida halimar basu dawo ba ne momyn tace wllh
kuwa kinga har yanzu basu dawo ba. maryam tace
uhm nidai na tafi karna makara sai na dawo bye
bye tafita tana tafiya tana tilawa dan karta manta
karatun da sukayi jiya sai ji tayi mota ta faka ta
gefan ta da yake dan titin yau weekend ba jama'a
sosai duk ana gida ana hutu wasu kartai biyu suka
fito a motar cikin hanzari suka kamata suka rufe
mata baki sannan suka jefata cikin mota sukayi
gaba da ita sunata tafiya kamar bazasu tsaya ba ita
kuma kuka take har ta gaji tayi shiru sai kuma ta
fara ajiyar zuciya. wayar ogan yan daban ne tayi
kara ya daga ya risina yace oga an cika aiki ga
yarinyar da ka ce mu kamo ta yanzu ma muna tare
da ita. kome ogan yace mai oho jinayi yace ok sir
ya kashe wayar ya mayar aljihu sannan ya juya ya
kalli yarinyar da idanun ta duk sunyi jawur yace
kuba marar kunya ba zaku gane kun tabo wuta mun
kashe dayar sannan kema an bamu umarnin mu
kashe ki amma ba zamu tashi a tutar babu ba sai
mun danaki tukun nan zamu kashe ki. hannu ta
dora a kai ta fasa wani uban iho hade da kuka.
wuka yaciro yace sheet yi mana shiru, kallo daya
zakawa mutumin ka gane bashi da imani gashi baki
ga wasu jaja yan idanuwa fuskar nan tashi ba
annuri sai kace hata damusa maryam kuwa ta kara
kankame jikin ta tana kuka ciki ciki ana cikin tafiyar
ne naga sun faka motar kome ya faru oho sun fito
duk su ukun ba mai fara'a a cikin su dayan naga ya
zagaya baya sannan ya dawo yace oga akwai
matsala fa munyi faci a bayan nan ogan ya daka
masa tsawa maryam dake cikin mota har dan
fitsari ya kufto mata dan tsananin tsora lol. ogan
yace bazaka kunce tayar ka koma baya wancan
dan garin ka wo mana faci ba ka tsaya kana wani
yen yen yen wuce daga nan dallah. cikin hanzari
naga wanda ake kira kumurci yaje ya fara kunce
tayar ya sabe ta akafada ya koma baya wato garin
da suka wuce to gashi dare ya fara yi shi kuma
ogan ya dauki gallan yace wa wanda ake kira da
mugu yace kai zanje wancan gidan man wanda
muka wuce a baya zan je in karo mai dan ina
tunanin wannan bazai karasa damu kano ba
sannan yace ka kula da wannan yarinyar sosai
kuma kasa ido a kanta sosai yace angama oga shi
kuma ya juya ya fice ya bi bayan kumurci suna
tafiya shi kuma ya shiga gaban mota ya kuna
music yana yi yana girgiza kai yana rawa ita kuma
maryam tunanin tserewa take yi sai sake sake take
yi can sai naga tayi a jiyar zuciya ko me ta tuna
oho nima cewa nayi my queen me kika tuna………
Naku   bigboy > whatsapp no 08096831009







→BANI NA KASHE TABA← PART 5
na bigboy isah
jakar ta naga ta bude ta ciro wani lacasera mai
sanyi kuma sai naga ta dakko wasu kwayoyi cikin
hanzari ta zuba a cikin kwalbar lacasera din shi
kuma mugu yana can yana jin music din sa har ya
manta tsaron mutum yakeyi can sai naga maryam
din ta dan matso tace bawan allah dan allah zan
sama breadi ko rabi ne zan dan hada shi da
wannan ne ince sai ta dago lacasera haba baaban
yana ganin lemo gashi dama yunwa yake ji ya
kwace kwalbar tare da cewa yar iska waya ce miki
yara suna shan irin wannan miko shi yana amsa
yaji da dan sanyi sanyi kuwa ya kafa kai sai da ya
shanye shi kaf sannan ya yi wurgi da robar
lacasera din waje ya juya ya kalle maryam yace ina
sauran nan take idan shi suka fara lumshe wa
kamar wanda yasha ya bugu. ita kuma a zuciyar ta
karku so kuga farin ciki sai dadi take ji.sai a lokacin
na kula ashe maganin barci ta zuba mai mutumin
ku ya langabe kai ya fara sharar barci hada
minshari. maryam din tana ganin haka sai ta bude
motar da sauri ta fito ai kuwa tace kafa me naci
ban baki ba nan ta ari ta kare tayi cikin daji da gudu
su maryam anga mutuwa saida tayi gudu 5 mint
sannan ta sama wani gidan fulani gari ne karami
duk yan filo ne a garin ji sai daka ake yi can kuma
anyi wa wani daga cikin yaran fulanin biki an dakko
makadi sai cashewa akeyi. alamarin su ogan yan
daba kuwa tare suka taho shida kumurci sai wajan
magari ba suka dawo tun daga nesa suke jin music
na tashi a cikin motar su ogan yace kutt lalai
wannan yaran zai ci uban sa har ya sama damar
kunna waka a motar nan kamar motar uban shi
zaici uban shi bari mu karasa tun daga nesa
kumurci yace oga yarinyar nan fa kamar bata mota
a fusace ogan ya juyo yace zan mare ka dan
ubanka kasan abunda kake fadi kuwa. to ka muna
shiru ai kuwa suna karasa wa sukaga mota wayam
ba maryam sama ko kasa can gidan gaba kuma
mugune sai sharar barcin sa yake tuna ogan yaje
ya bude gidan gaban ya kwada ma mugu mari.
cikin barci ya tashi yana iho yana wllh na tuba
bazan kuma ba. yana ta yan surutan shi dai ogan
ya daka masa tsawa wanda ni kaina saida na
zabura saura kadan in yarda wayar in gudu lol.
amma saboda tsabar juriya irin tawa tsayawa
kawai zan yi anan *************
ku sani wannan abunda ya faru da maryam kanwar
deeny ka sancewar itama tunda ta fita islamiya
bata kara dawowa ba…………Naku   bigboy > whatsapp no 08096831009


mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group
bigboy
on-line 15.04 08:12
→BANI NA KASHE TABA← PART 6
na bigboy isah
tsawar da ogan ya mai ita ce ta dawo da shi
hayyacin sa ogan jikin murya mai kara yace ina
wannan yarinyar?. nan fa mugu ya fara kame kame
yana. dama uhmm uhmm ogan yace dama me
bazaka fada ba saina rabama kai biyu ogan ya fiddo
wukar shi yace wllh kayi wasa zan raba maka kai
biyu. jikin mugu na rawa yace oga inaga sayan
lacasera ta biku baku hadu a hanya ba ni dai na san
na kwace mata lacaseran ta ina shanye wa barci
ya kwashe ni ban farka ba sai ynz wllh oga. nida
nake gefe dariya na kama yi ma mugu. tsawar da
ogan ya sake yi ita tasa na kama baki na nayi
shiru. ogan yace kasan me kake fada kuwa kana
nufin ta tsere yanzu kasan ko asarar nawa ka jawo
mana kuwa ga asarar yarinyar sannan ga na 3m
naira ogan ya jingina kai jikin mota yana wani huci
kamar zaki. shi kuma kumurci da yake gefe ji
sukayi yace alhamdulilah su duka suka kalle shi
yace oga yadda zamuyi kawai muhau motar mu
muyi gida tunda dama mai gida yace a kashe ta to
kaga kawai sai mu koma muce angama aiki duk
mun kashe su tunda kaga wannan yarinyar dai
bazata iya tafiyar da zata sama gari a cikin wannan
daji ba nasan zatai ta yawo ne har yunwa ta kashe
ta kaga mun cika aiki kenan HAHAHAHAHAHA
dariyar mugun ta ogan yayi sannan kamar hadin
baki su duka suka dauka HAHAHAHAHAHAHAHAHA
sai dariyar suke *************
maryam kuwa zuwa tayi wajan masu kade kadan
nan ta zauna ta fara tunanin maganar ogan yan
daban nan da yace mata mun kashe dayar saura ke
ita a tunanin ta to wacece dayar? amsar data kasa
bawa kanta kenan ta dago kanta sai kalle kalan
yaran fulani take can ta hangi wani bakin maciji ya
doso wajan wasu yan mata su biyu dake zaune a
gindin wata bishiyar bedi da gudu ta nufi wajan su
tana kutashi maciji maciji suma da gudu naga sun
watsa suna iho aradu mashiji aradu mashiji kafin
kace me samarin fulanin nan sun rufe macijin da
duka dama kunsan basa rabuwa da sanda ga kuma
wuka. ita kuma yar fulanin zagayo wa tayi tana
neman maryam data taimaka musu can ta hango ta
a inda take zaune da ta kuma yin tagumi abunta a
hankali yar filo ta matsa wajan ta a tsorace tace
hannuka ko maryam ta dago kai tace yauwa
sannun ki sannan yar fulani tace amma naga
kamar kai bako ne anan ko ko zaka iya fada min
sunanka? ita kam maryam abun ya daure mata kai
an maidata namiji bata san haka suke maganar su
ba mace a maida ta namiji namiji kuma a maida shi
mace. can dai maryam ta dago kai ta kalli bafula
tana tace nifa macece ba namiji ba kuma sunana
maryam. sai bafulata nan ta kwashe da dariya tace
kayi hakuri haka maganan mu take. taci gaba da
cewa ni sunana aneesat amma mutanan rigga nan
suna cemin anne. maryam tace gud nice name
aneesat. ita kuma anne budar bakin ta sai cewa
tayi kice naman aneesat lol. maryam ta kwashe da
dariya tace cewa nayi nice name. ina nufin sunan
yayi dadi sannan annee tace ohho hk kike nufi
kenan. haka dai suka ci gaba da hira tamkar
kawaye. wanda suka saba da juna can dama. dan
itama anne har waje ta samu ta zauna sai labari
suke maryam na mata dariya yanayin hausar su ta
fulani. anne tace………
mu hadu a whatsapp→ 08140027062 Group
maman sabir
on-line 15.04 14:45
mungode
mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group
delete
bigboy
on-line 15.04 15:27
→BANI NA KASHE TABA← PART 7
na bigboy isah
anne tace wai shin gidan suwa kika zo ne awannan
riggar tamu?. maryam ta sunkuyar da kai sannan
sai hawaye suka kwararo mata. tace sato ni akayi.
nan ta kwashe labarin duka ta fadawa aneesa.
anne tayi mamaki dajin wannan labari. ta gyada kai
tace tabb aradu kinyi gudun mutuwa. ko kin san
daga nan zuwa bakin titi tafiyar wuni guda ce kuwa
gamu wanda muka saba ma kenan. maryam ta
bude baki tace wuni guda fa kika ce?. annee tace
kwarai kuwa. maryam tace allah ne kawai ya cece
ni daga sharin su. anne tace yanzu kinga dare yayi
tashi mu tafi gida sai mu kwana tare. maryam tayi
godiya ta tashi suka tafi.**************
acan kuwa gidan kawu, kawu ne yake cewa wai ni
shin da ake cewa deeny yayi kisan kai wa ya
kashe?. hawaye ne suka biyu ta kan fuskar maman
deeny sannan tace gawar halima aka gani a motar
shi sannan gawar halima aka samu a cikin nan ta
kara fashewa da kuka. maman aliyu ce ke rarashin
ta tace kiyi hakuri yanzu tashi mu tafi gidan br
fadila din dakyar aka samu tayi shiru ita dai abun
ya mata yawa ba maryam ba zaharadeen din ta
tasa mayafi suka fita suka tsaida nafen sai gidan
barrist fadila. sunyi sa'a tana gida kuwa da yake ba
wani aiki suna isa ta tare su hannun bibiyu tasa mai
aiki ta kawo musu abinci da ruwa da lemo haka
kuwa aka kawo musu abinci aka girke a gaban su
ga lemoka kala kala. su duk hankalin su ba'a akan
abince yake ba su brfadila suke su ta fito su mata
bayani kawai. can after 5mnt sai gata ta fito daga
daki fuskar ta cike da murmushi tace a su maman
deeny manya ba'a ko ganin ku yanzu yaushe rabo
mu hadu. maman deeny kuwa murmushi ta nema
ta rasa duk batada sukuni. tace ai kune manya
bakwa ko neman mu. kallo daya brfadila tawa
maman deeny ta fahimci ba lafiya ba. taga duk ta
wani canza. tace maman deeny lafiya kuwa. haba
sai hawaye kamar jira suke dama nan ta kwashe
labarin duka ta fada wa barrist fadila sannan tace
yanzu haka sunce gobe gobe za'a shiga kotu
saboda baban halima ya kai kara. brfadila wani a
jiyar zuciya ta saki sannan tace tabdi babbar
magana. tace yanzu bari in shirya inje mu gana da
deeny inji kan lamarin ankama deeny ai bamuga ta
zama ba. maman deeny ta dan share hawaye
sannan ta kalla brfadila tace yanzu saiki fada mana
abunda zamu kawo dan allah ki ceci yaran nan
nasan bazai iya kisan kai ba kuma shike daukar
dawai niyar mu yanzu in bashi ya zamu yi gashi
maryam din ma bamu san inda tayi ba. cikin sauri
fadila ta dago kai ta dafe kirji tace maryam ta bata.
maman aliyu ce ta bata amsa tace kwarai kuwa tun
jiya data fita islamiya bata dawo ba har yanzu.
maman deeny kuka take sosai. fadila ta kalle su
cike da tausayawa ta taso daga kujerar ta ta dawo
kusa da maman deeny ta rike hannun maman
deeny sannan tace. ki kwantar da hankalin ki
isha'alahu zamuyi nasara kuma kibar maganar kudi
deeny ai dana ne sannan ta kara dacewa in allah
yayarda deeny zai fito ki bar komai a hannun na
yanzu zanje na sama deeny. maman deeny da
maman aliyu godiya suke kamar me sun rasa kalan
godiyar da zasu mata ma. tace ba komai muje
driver ya kai ku idan ya dawo sannan na shirya sai
mu wuce da shi station wajan deeny…………
mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group
bigboy
on-line 15.04 15:28
→BANI NA KASHE TABA← PART 7
na bigboy isah
anne tace wai shin gidan suwa kika zo ne awannan
riggar tamu?. maryam ta sunkuyar da kai sannan
sai hawaye suka kwararo mata. tace sato ni akayi.
nan ta kwashe labarin duka ta fadawa aneesa.
anne tayi mamaki dajin wannan labari. ta gyada kai
tace tabb aradu kinyi gudun mutuwa. ko kin san
daga nan zuwa bakin titi tafiyar wuni guda ce kuwa
gamu wanda muka saba ma kenan. maryam ta
bude baki tace wuni guda fa kika ce?. annee tace
kwarai kuwa. maryam tace allah ne kawai ya cece
ni daga sharin su. anne tace yanzu kinga dare yayi
tashi mu tafi gida sai mu kwana tare. maryam tayi
godiya ta tashi suka tafi.**************
acan kuwa gidan kawu, kawu ne yake cewa wai ni
shin da ake cewa deeny yayi kisan kai wa ya
kashe?. hawaye ne suka biyu ta kan fuskar maman
deeny sannan tace halima aka gani a motar
shi sannan gawar halima budurwar aka samu a cikin motarsa nan ta
kara fashewa da kuka. maman aliyu ce ke rarashin
ta tace kiyi hakuri yanzu tashi mu tafi gidan br
fadila din dakyar aka samu tayi shiru ita dai abun
ya mata yawa ba maryam ba zaharadeen din ta
tasa mayafi suka fita suka tsaida nafen sai gidan
br fadila. sunyi sa'a tana gida kuwa da yake ba
wani aiki suna isa ta tare su hannun bibiyu tasa mai
aiki ta kawo musu abinci da ruwa da lemo haka
kuwa aka kawo musu abinci aka girke a gaban su
ga lemoka kala kala. su duk hankalin su ba'a akan
abince yake ba su brfadila suke su ta fito su mata
bayani kawai. can after 5mnt sai gata ta fito daga
daki fuskar ta cike da murmushi tace a su maman
deeny manya ba'a ko ganin ku yanzu yaushe rabo
mu hadu. maman deeny kuwa murmushi ta nema
ta rasa duk batada sukuni. tace ai kune manya
bakwa ko neman mu. kallo daya brfadila tawa
maman deeny ta fahimci ba lafiya ba. taga duk ta
wani canza. tace maman deeny lafiya kuwa. haba
sai hawaye kamar jira suke dama nan ta kwashe
labarin duka ta fada wa barrist fadila sannan tace
yanzu haka sunce gobe gobe za'a shiga kotu
saboda baban halima ya kai kara. brfadila wani a
jiyar zuciya ta saki sannan tace tabdi babbar
magana. tace yanzu bari in shirya inje mu gana da
deeny inji kan lamarin ankama deeny ai bamuga ta
zama ba. maman deeny ta dan share hawaye
sannan ta kalla brfadila tace yanzu saiki fada mana
abunda zamu kawo dan allah ki ceci yaran nan
nasan bazai iya kisan kai ba kuma shike daukar
dawai niyar mu yanzu in bashi ya zamu yi gashi
maryam din ma bamu san inda tayi ba. cikin sauri
fadila ta dago kai ta dafe kirji tace maryam ta bata.
maman aliyu ce ta bata amsa tace kwarai kuwa tun
jiya data fita islamiya bata dawo ba har yanzu.
maman deeny kuka take sosai. fadila ta kalle su
cike da tausayawa ta taso daga kujerar ta ta dawo
kusa da maman deeny ta rike hannun maman
deeny sannan tace. ki kwantar da hankalin ki
isha'alahu zamuyi nasara kuma kibar maganar kudi
deeny ai dana ne sannan ta kara dacewa in allah
yayarda deeny zai fito ki bar komai a hannun na
yanzu zanje na sama deeny. maman deeny da
maman aliyu godiya suke kamar me sun rasa kalan
godiyar da zasu mata ma. tace ba komai muje
driver ya kai ku idan ya dawo sannan na shirya sai
mu wuce da shi station wajan deeny…………
08096831009




→BANI NA KASHE TABA← PART8
na bigboy isah
salama tayi ya amsa kanshi a kasa yanata faman
zubarda hawaye duk wanda yaga deeny a wannan
halin dole ya tausaya masa sbd tsananin duka da
yasha. takare mai kallo sannan ta sama waje ta
zauna tace sannu deeny da kyar ya dago kai ya
kalle ta yace yauwa sannu sannan tace sunana br
fadila nice lauyan ka mai kare ka ina san sannan
wasu bayanai game da abunda ake zargin ka da shi
da fatan ka shirya?. shidai kawai ido ya zura mata
sannan ya daga kai alamun eh. nan sukayi yan
maganganun su tana tambayar sa yana bata amsa.
daga karshe tace zamuyi nasara isha allahu kafin
nan ina so in sanar da kai cewa karka yi magana
biyu a kotu dan hakan zai iya jawo mana matsala
yace toh sukayi sallama ta tashi ta fice.
***** alhj sunusi kuwa wani kwararan lauya ya
nema ana ce dashi barristr bashir ya biya shi kudi
har 500,000naira da yake shi ya kasan ce mai kudi
ne kudin sa kuwa sanadin wani yayan shi ya,same
su wani compny da yayan ya bar mishi sunan
yayan nashi alhaji bashir matar shi daya saratu. da
daya allah ya basu sunan yaran nasu yazeed yaran
nasu yana jida kudin uban sa shi kuma uban ya
sakar mai duk dukiyar sa a cewar shi shi zai gaje
shi ay hajj saratu taita fada idan taga yanda alhj ke
sakar wa dan nashi kudi.
*******
wata babbar kotu nagani a cike makil da yan kallo
da wanda aka bukaci ganin su. kotu tayi shiru.
alkali kawai ake jira ba'a jima ba saiga shi ya shigo
ai kuwa duk jama'a gaba daya aka mike alkali ya
nufi set din sa ya zauna .an fito da zaharadeen
cikin ankwa duk wanda ya kalle sa saiya tausaya
mai alkali yace assalamu alaikum warahmatul lahi
wabarakatuho.
duk jama'a suka amsa sannan alkali yaci "court
clerk call the
case" Court yafara bayaninsa "In the case of
murder between zaharadeen kabir and alhj sunusi.
yaci gaba da bayanin sa muna bukatar lauyoyi su
gabatar muna da kansu. ya koma ya zauna. my
name is barrister bashir lauyan mai kara shima ya
koma ya,zauna.fadilat ta mike my name is barrister
fadila mai kare wanda ake tuguma. sai duk kotu
tayi tsit har yan wajan ma kowa yayi shiru. babu
wanda bai hallara a wajan ba.maman deeny.amina
maman aliyu.alhj sunusi da matar sa. da wanda
yaga gawar da duk sauran jama'a dai duk sun
halara har da baban yazeed da maman sa duk…………08096831009








→BANI NA KASHE TABA←PART 9
na bigboy isah
br bashir ya nema alfarma ga kotu domin ya fara
tambayoyin sa. kotu tamai izini. sannan yaje gaban
deeny. yace zanso sanin cikeken sunan ka. ya
dago kai yace. sunana zaharadeen kabir. br bashir
yace. miye hadinka da halima. deeny yace budurwa
tace. duk jama'a suka dago kai suka kurawa deeny
ido.kai ka kashe halima?.deeny yace BANI NA
KASHE TABA. br yace an tabbatar da anga gawar
halima a motar ka muna da sheda ba daya ba ma.
yace haka ne. br yayi ajiyar zuciya. sannan yace to
waya kashe ta?. deeny yace nima ban sani
ba.bashir yace zaka iya fada mana dalilin ka na
cewa bakai ka kashe taba kuma bayan antabatar
kai kazo har gida ka dauke ta?. deeny ya fara bada
labari. ranar washe garin ranar da dare mu kayi
waya da halima take cemin dan allah gobe inzo mu
tafi yawan shakatawa ita kafin hutun su ya kare
tana so ta dan ga gari. da har naki amincewa nace
ni ba inda zani yawan shakatawa ay na masu
kudine muda muke nema ina mukaga samun damar
zuwa wani shakatawa. ai kuwa nan ta fashe da
kukan shagwaba wai ita wllh sai yazo ya dauke
ta.dai dai nan hjj hauwa ta shigo dakin halima ta
isketa da dan kukan ta hada hawaye. da sauri ta
karasa tace halima lafiya kuwa.tace momy lafiya
lau ba komai. hjj hauwa tace ban yarda ba sai kin
fada min. alokaci shi deeny kuwa yana saurarn su.
sai halima tayi sauri ta katse call din ta kamo wani
video fassara tace momy fin ne nake kallo shine
abun ya bani tausayi nake hawaye. momy dariya
tayi tare da cewa allah ya shirye ki. sannan ta
kama hanya ta fita. tana fita daga dakin. halima ta
sake kiran deeny duka daya ya daga wayar kamar
dama jira yake. yana dagawa yace kin gama
kukan. tace pls dan allah kayi hakuri kazo mu fita
gobe. yace kwantar da hankalin ki gimbiyata zanzo
isha'alahu ai kuwa dan murna hada tsale sannan
tace gobe karfe 10 ka shirya ko anguwar mu
sannan baban na ya fita nasan yada zanwa momy
ta barni in fita kaji yace to.allah ya kaimu haka taita
jin dadi. har allah allah take gari ya waye. ai kuwa
gari na waye wa ta yi sallah ta fito farllo sukayi
breek sannan momy ta dakowa dady jakar sa zai
fita dan har ya makara yanzu karfe 9:30 suka raka
shi har mota halima ce rike da jakar sai da ya shiga
mota sannan ta durkusa ta mika mai ya amsa yace
baby allah ya miki albarka tace amin sannan ya
juya yawa maman baby bye bye driver yaja shi
suka fice yana su kuma suka koma farllo suna
kallo ita kuma halima duk tabi ta damu ta rasa
wace karya zatayi ga waya a hannun ta sai
jujuyawa take. hjj hauwa ta fahimce ta tace ke me
yake damunki ne naga duk kin changer fuska.
halima tace momy mun dan sama sabani ne da
deeny wai shine yace inje yana kofa zai
bani.hakuri. momy tayi murmushi tace kude yaran
nan bakwa gajiya da rikici ko shiyasa naga jiya kina
hawaye. ta sadda kanta kasa. momy tace hmm
shiyasa naga bai shigo ba kenan yasan yau ba a
shirye kuke ba ay saiki tashi ki fita. halima
a,zuciyar ta cike da farin ciki a fuska ko kamar
bata so. ta tashi ta shiga dakin ta tayi yar kulleyar
ta sannan ta chanza kaya. wata atamfa ta saka mai
kyau green & water riga da siket sun mata cip cip
sun kara fito da kyan ta ta dau gyalan ta fari ta yafa
sannan taje jikin mirror ta kalla kanta tayi
murmushi sannan ta fice a dakin …………
mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group
bigboy
on-line 17.04 12:52






→BANI NA KASHE TA BA← PART 10
na bigboy isah
ta fito tace momy na tafi momy tace to a dawo
lafiya kuma kice ina gaida shi tunda shi yau bazai
shigo ya gaida mu ba. tace ameen momy zai ji.
ta fita da murnan ta ta nufi inda yake a mota ta bude
motar ta shiga sannan tayi ajiyar zuciya tace to sai
motafi ko ina zamu fara zuwa. wani kalan kallo ya
mata mai cike da so da kauna. yace saida kika
wahalar dani na zo sai jira nake kinki fitowa. ta
mararai raice tace haba sweethr kasan irin faman
da nasha kafin in samu a barni na fito kuwa sai da
nayi karya fa. gaba daya suka kwashe da dariya.
sannan yaja motar yayi gaba suna tafiya suna ta
zuba hirar su ta soyayya tana tamai shagwaba kala
kala tace wannan yatsaya ya saya tace wancan
haka dai suke ta tafiya suna soyayyar su abun
gwanin ban sha'awa. sune har wajan la'asar yace
tabari tunda ga masalaci a kusa kuma ankira sallah
to tabari yayi sallah tunda kinga ko sallahr azahar
banyi ba. tace to nifa nima ay banyi ba. yace ai ku
mata ne kun saba dama idan ana biki sallar huni
guda duk kuke hadawa lol. ta jefo mai bisket din
hannun sa ya kare da hannun sa kuma ya fita da
gudu yana dariya itama dariyar take. ita kadai a
mota shi kuma ya nufi masalaci ya dauki buta ya
zuba ruwa ya nufi ban daki.
kotu dai tayi tsit deeny kadai ake ji sai zuba labari
yake nima ina gefe ina sauraran sa.
yace bayan na gama sallah ne na nufi mota ina
zuwa na iske halima a kwance ni a tunani na barci
take haka nayi murmushi nace yarinya ai gobe
bazaki kara cewa a taho yawan shakatawa ba
gakinan duk kin gaji har kinyi barcin dole. ni kuwa
nace deeny ka kashe yarinya kace barci take ko
lol. yaci gaba da jan motar shi bai tsaya ko inaba
sai gidan su halima yana zuwa ya tsaya a kofa
yakama dan babuga ta yana cewa my luv tashi
mun iso my heart ki tashi ko duk gajiyar ce haka.
yayi yayi yaga ko motsi taki yi. nan fa duk ya rikice
ya shiga gida ya kira mai gadi wai yazo ya tada mai
ita ta shiga gida. ni duk a sannan ban fahimci
halima mutuwa tayi ba inji deeny. mai gadi yazo
yace ban gane in taya ka tadata ba mai ya faru.
deeny yace nidai nayi nayi taki tashi kuma daga yin
barci. mai gadi ya matsa kusa da ita ya kama
hannun ta ya daga ya sake shi yaji hannun ya dawo
kamar dai yadda gawa take. shima duk bai gamsu
ba tukun ya bude idan halima yaga fari fat ai kuwa
dama tsoho ne da gudu ya ban kade deeny ya nufi
cikin gida.deeny har zai bishi sai yaji mai gadi na
cewa hajiya ya kashe miki yarinya…………
mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group
bigboy
on-line 18.04 18:45
→BANI NA KASHE TABA← PART 11
na bigboy isah
deeny da gudu yayi baya duk jikin sa na rawa ya
fizgi mota yayi ciki gudu yake ba kaf kaftawa yace
ban tsaya ba nabi wani barji a tunani na duk wajan
daji ne ba mutane. yace haka na je na tsaya da
mota na juya ina ta kallan halima ina kuka a zuciya
ina cewa wai yanzu halima ta ta mutu kenan. nan
hawaye suka fara zarya a fuskata na fito na dauki
halima. wai ni a nufina binne ta zanyi idan na koma
gida koma me za'ayi sai ayi. ina tafiya inata sake
sake na dan yi nisa da mota ta nan na ajiye halima
inata kuka ina jijigata ina cewa ki tashi ki tashi.
shiru nine har magariba ina wajan nan fa na gaji sai
kawai na fara haka rami da yake wajan ba tauri nayi
rami mai dan tsawo nan kuma sai na tsaya ina
tunani toh in binne ta anan ko kuma in maida ta gida
a mata sallah a sa mata lukafani. inata saka
wancan kunce wancan. sai ji nayi ance waye nan
ban ankara ba sai ganin kibiya nayi a gaba na ta
caki kasa ina juyawa naga wani saurayi ne ya
durfafo ni hannun shi rike da kwari da gwafa. ashe
wai nan garkar rogwan sune wai yana ce ni
barawan rogo ne lol. da gudu na bar waje nayi
wajan motata sai na danyi gudu kadan sai na tsaya
a zuciyata nace gwara in tsaya in cemai yar uwata
ce ta mutu shine zan binne ta. wata zuciyar kuma
tace wannan da yake fada a kan rogo baya ko
tsayawa a mai bayani toh ina zai tsaya sauraro
na.yana cikin hakan sai ganin mutum yayi a guje ya
nufo shi yana barwo aradu barawo ne. ni kuma sai
nake cewa ka tsaya ka saurare ni. haba ba sai ji
nayi ya sako wata ki biyar ba badan na guce ba da
sai ta same ni. da gudu na fada mota naja ta da
gudu ya biyo ni. yana har bi yana jifa har dai na
samu na tsere. can naje bakin titi na ajiye motar
sannan na taho a kasa sai dai ina fargaba amma a
haka nace kai gwara inje duk abunda zai same ni
ya same ni amma sai na dako halimata na nufi
garkar na dan bi a hankali na leka nayi zatan yana
nan. amma sai naga wayam tun a nesa naji gabani
yana faduwa da na hangi wajan da na ajiye halimata
ba komai a hajan tun a nesa na dora hannuwa a kai
ina isa wajan kuma na iske ba komai a wajan sai
dai ga dan ramin da nayi nan. haka nata ratsa daji
ina neman saurayin nan ko sama ko kasa na
nemeshi na rasa. bana jin kukan komai a wajan sai
kukan tsintsaye da na dabobi da yake dare ne
rananr dai haka nata yawo ina kuka kamar
mahaukaci ina tunanin shikenan na rabu da
masoyiyata abar kaunata hasken zuciyata bugwan
zuciyata. na fashe da kuka a ranar duk wani tsoro
ya fita a raina bana jin ko tsoran duhun dajin nan
haka na hakura na koma naja mota na inata tunane
tunane. na nufi gida…………
mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group
.




bigboy
on-line 19.04 09:54
→BANI NA KASHE TABA←PART 12
na bigboy isah
TUN DAGA BAKIN KOFA naji gabana yana faduwa
duk tsoran maman mu nake. sai kuma nayi tunanin
ay bata san komai ba. kawai na shiga gida na nufi
daki na na kwanta. banyi barci ba har safe da
asuba nayi sallah a daki dumin bazan iya fita ba duk
na gaji saboda yawan da nasha jiya a daji ina gama
sallah na nufi dakin momy ai kuwa ina isa kamar
ance mata gani nan sai saukar mari naji tass tace
ina kakai musu yarinya nasan bazaka iya kisa ba
amma ina kakai.musu yarinya.nace mama wllh
BANI NA KASHE TABA momy ta zaroo ido dagaske
ta mutu. ai kuwa ta shake min wuya tana cewa. me
yasa kakashe ta me tama kane da zaka kashe
musu ita banyi zatan zaka iya kisan kaiba
zaharaddin sannan ta sake ni daga shake min
wuya da tayi idanuna duk sun cika da kwala. momy
ta koma gefe tana kuka. a hankali na durkusa nace
momy wllh BANI NA KASHE TABA ana nan yan
anguwa suka zo zasu toya mu sannan police suka
kore su aka kamoni akayo nan dani. ya mai girma
mai shari'a wllh gaskiyar abun da na sani
kenan.mustapah ne yace yallabai wannan ba abun
kamawa bane idan kayi la'akari da maganganun sa
akwai karya a ciki sannan yace na gode ya mai
shari'a. sannan alkali bayan yagama yan rubuce
rubucen shi yayi aziyar zuciya sannan yace
barrister fadila fa tana da tambaya. tamike tace
akwai ya mai shara'a. tace ina rokon kotu data bani
izini in kira hjjy karima maman deeny.alkali yace an
baki izini. ana bukatar ganin hjj karima maman
deeny. ta taso taje ta tsaya a inda aka tana.br
fadila tace da farko muna bukatar jin sunan ki dana
mijin ki.ta goge dan hawayan dake fuskar ta domin
ta tausayawa yaran nata. tace sunana karima mata
ga alh kabir . fadila tace wannan fa danki ne
kokuwa dan riko ne. maman deeny tace dana na
cikina. fadila tace maganar da ya fadi duk gaskiya
ne haka sun faru. maman deeny tace duk abun da
ya fada dangane da ni haka ne. tun safe ko karin
kirki baiyi ba yace min zashi gidan su halima da
yake ni nasan tsakanin su shiyasa ban tugume shi
mai zaiyi a can din ba. haka naita jiran shi amma
shiru bai dawo ba kanwar shi ma kuma haka da ta
dawo daga school ta takura min da tambaya ina
yaya deeny sai dai nace ya tafi gidan su halima. da
yake itama halimar kawar ta ce.har tayi shiri
makarantar islamiya amma deeny bai dawo ba
abun ya daure mana kai gaba daya. yaran da yake
cin abincin rana a sai gashi har 3:30 bai dawo ba.to
bayan fitar maryam ne ba'a jima ba sai ga mai
gadin gidan su halima da yan sanda wai sun zo
kama deeny anan ne suke shaida min wai ya kashe
halima. na dafe kirji sakamakon hani mumanan
faduwar gaba da naji. sannan na fada musu rabona
da shi. amma basu hakura ba suna ce boye shi
nayi duk saida suka har gitsa gida suka shiga ko
ina amma basu samai ba. suna gidan tun lokacin
har bayan isha'i amma bai dawo ba. ni kuwa abun
duniya ya isheni dan a lokacin har jini na ya hau.
saboda yada abun suka min biyu ga deeny ana
zargin shi da kisan kai sannan ga maryam bata
dawo ba. hakan yasa na shiga daki na kwanta
zazabi ya rufe ni ban tashi ba sai da safe………………08096831009












→BANI NA KASHE TABA← PART 13
na bigboy isah
barrister fadila. tace mun gode. zaki iya komawa
mazaunin ki. sannan br fadila tasa akata kira
mutane daya bayan daya. daga kan maman halima
har mai gadi duk wanda labarin deeny ya shafa. sai
yace eh maganar da ya fada gaskiya ce. barrister
fadila. tace ina rokon wannan kotun mai adalci data
rike labarin wannan bawan allah karta dauke su a
karya. bayan ga shaidu mun samu kuma duk sun
tabbatar da zancen sa haka ne. sannan ina rokon
kotu da ta tura jami'a tsaro dumin su tafi da deeny
ya kaisu har wannan wajan da yayi rami dan
tabbatar da gaskyar sa. na gode ya mai shari'a.
deeny kuwa duk ya tsure dumin a lokacin bai san
ma inda ya tunkara ba balle ya kai wanda za'a hada
shi da su yanzu. turkash. alkali yace munji kuma
mun yarda da zan can ki barrister fadila gobe za'a
hada shi da jami'an tsaro dumin su je su bincika
dan tabatar da gaskiyar sa sannan mun dage
wannan zama har zuwa jibi. alkali ya buga
gudumarsa…………kotu ta watse >>>>> cigaban labrin deeny>
lokacin da dan fulani ya dawo wajan sai ya tarar da
mutum a kwance kuma ga duk kan alamu wancan
da ya kora binne wannan din yazo yi. adan tsorace
ya nufi wajan a hankali ya juyo ta sai yaga ashe
macece ma daya kula sosai sai yaga da sauran rai
da sauri ya sabe ta ya nufi gida da zuwa kuwa
gwaggo ta tarye shi suka kamata suka ajiye a kan
wani gadan kara ita kuwa har yanzu bata dawo
hayyacin ta ba. nan gwaggo take tambayar isah ina
ka samu wannan yarinyar gata kamar yar bunni.
tana dan jujuyata.isah yakwashe duk labarin
abunda ya faru ya fadawa gwaggo gwaggo tace to
hike nan allah hukumusa'a. ya tashi yace gwaggo a
kula da shi ni na komai dawa. da yabi kwari da
gwafan shi yayi ciki.
da sasafe halima a hankali ta bude ido ta ganta
cikin bukka tayi mamaki sosai. a hankali ta taso
jikin ta ba kwari. tana tagal tagal. gwaggo ta taho da
gudu ta tare ta daga faduwar da zatayi. ita kuma
halima deeny take ta kira tana ina deeny na. deeny
nan inane. duk ta wani rikice. gwaggo tace kiyi
hakuri mana ki saurare ni nan ba garin ku bane.
nan kina cikin rugga ne. halima ta zaro ido rugga
kuma. gwaggo tace tabbas kuwa. jika na ne ya
tsunto ki jiya a can garkar su wani na kokarin binne
ki. halima tayi ajiyar zuciya tace yanzu ko wane
hali mamana da abbana suke cikin. hawaye kawai
suka shararo mata. gwaggo tace jikin ki ba kware
muje ki zauna. ai kuwa haka gwaggo ta taimaka
mata a hankali taje ta zauna…………>
mu hadu a https://m.facebook.com/groups/1232550283531628.


 whatsapp→ 08096831009 Group
bigboy
on-line 21.04 11:05
→BANI NA KASHE TABA← PART 14
N@ BIGBOY isah
acan kuwa bangaran maryam tashe sukayi suka
nufi gidan su anne. suna shiga suka iske iyayan
anne a tsakar gida suna hutawa suna yar hirar su.
suka karasa maryam ta gaishe su suka amsa cikin
fara'ar su sannan maman anne tace aneesat
wannan fa daga ina haka kamar yar bunni. anne
tace yar bunni ce mana yan fashi ne suka sato
ta,zasu kashe ta shine ta tsero har allah ya kawo ta
nan kuma a dandali muka hadu tataima ka mana ta
nuna mana maciji zai sare mu. shine har nake
tambayar ta gidan suea tazo sai ta bani lbr shine
nace bari muzo nan gidan ta kwana kafin akaita
garin su.abban anne yayi murmushi yace allah ya
miki albarka kinga dadin zaman birni kenan yaci
gaba da cewa ni naso in sama kudi ma a wannan
shekarar mu koma birnin nan mu duka har gwaggo
da yayan ki ya kalle anne. maman anne tace wllh
malam ba inda zaka halan kaje ka likewa wata kace
auranta zakayi ko wllh baza mu ba toh. su anne
gaba daya suka kwashe da dariya har maryam
dariyar take. ai kuwa sai gani nayi. maman anne ta
tashi ta shiga bukar su. nan anne da maryam da
baban maryam sukaita hirar su. maryam kuwa ta
saki jiki.baban anne yace aneesat tashi ku tafi daki
kusha fura sai ku kwana daki daya keda bakuwar
taki ko. anne tace to abba. suka shiga dakin daga
wani gadan kara bazai ci mutum uku ba na mutum
biyu ne ko katifa babu sai tabarmar da aka shin fida
da kuma barguna. da yake anne mai tsafta ce dakin
yar bukkar tata tsaf tsaf da ita. gefe kuma ga yar a
kwatin ta. hada nunawa maryam wai yayan tane ya
sayo mata. kuma duk ruggar nan babu mai kalan
ta. maryam kuwa me zatayi banda dariya. taga an
dakko wata tsohuwar akwati wai nan abu mai
daraja ne a garin. nan dai suka gama shirman su
suka gaji da hira suka kwanta. ai kuwa ranar da
dare maryam tasha jifga.daga anjima sai dai taji an
laf to mata kafa ta janye ana jimawa ta kara jin an
wullo mata. maryam tace na shiga uku wannan
kamar mage dai wannan ai mijin ki ya shiga uku. a
haka dai har asuba tayi. maryam ta tashi ta fito ta
dauki buta dama annee ta nuna mata bandaki. ta
fito tayi alwala. sannan taje tayi sallah tayi
adda'au. nan fa ta fara tunanin maman ta da kuma
yaya deenyta. tana cikin wannan tunanin taji matsin
anne ta farka ta murge ido taga maryam a kan
sallaya. tana kallan ta. tace ke kuma haka ake a
garin ku kita shi kiki tada mutane ko. maryam tace
ke tada ki ai sai jirgi ko kuma azo da bulala. anne
tace to miyasa baki dakko bulalar ba. maryam tace
ba komai ai akwai gobe. da sauri anne tace toh
gobe me zakiyi?. tace ahah bulala zan samo mana
saboda tada ki ba kince mi isa ban samo bulala ba.
anne tace wasa nake miki kinji yar kawata. ai
wannan lalausan jikin nawa bazai dauki bulala ba.
gaba daya suka kwashe da dariya. maryam tace.
katashi ka nema ruwa ka yi alwala kazo kayi
sallah. anne tace kai abun hada tsokala ai dai
allahn da yasa ni maganar fulanin ma bata kama
baki na ba.kinsan mu a burni muka girma. maryam
tace wai ina wannan yayan naki yake ne. sai kira
kike yayan ki yayan ki. anne tace yayana yana
gidan gwaggo gwaggo ta kwace mana shi ay. tace
bari dai in tashi wannan hirar ba karewa zata yi ba.
ta tashi taje tayi alwala. ta dawo ta iske maryam
tayi tagumi sai tunani take. anne tace maryam
maryam.firgigit ta dawo hayaccin ta daga tunanin
da take. anne tace kinga indai gida ne ki kwantar da
hankalin ki. yanzu da muka gaisa da mamana tace
gobe zata bawa yaya isah kudin mashin ya maida
ki garin ku. cikin fara'a da murna tace wow na gode
na gode. sosai.sis.anne tace bari inyi sallah ki
rakani zan kaiwa su gwaggo abin kari. maryam
tace toh shikenan………<
mu hadu a  https://m.facebook.com/groups/1232550283531628     whatsapp→ 08096831009 Group
bigboy
on-line 21.04 11:08
→BANI NA KASHE TABA← PART 15
N@ BIGBOY isah
>tunda sasafe police uku tare da deeny suka hau
mota suka nufi daji shidai deeny ba zai gane
wannan garkar ba wacce yaje yayi rami haka sukai
ta shara gudu deeny na nuna hanya duk da ba gane
wajan yayi ba saboda da dadare ne shi sadda yazo
ana tafiya da ya hangi wasu garake can nesa yace
toh a tsaya aka tsaya aka firfito daga motar.
yansanda suka sa deeny a tsakiya har suka kunce
mai unkwar dake hannun sa wai a cewar su ya
za'a yi wannan dan yaran ya iya tserewa daga
hannun mu mu uku. ni kuwa dake gefe ido kawai
na zuba inga mai zai faru. haka sukai ta tafiya suje
wannan garkar suga babu rami deeny kuwa ya fara
tsurewa dan ya sare ganin ba'a gane karkar ba. a
haka suje wannan yace inaga wacan ce su kara
gaba yace la na tuna wacan ce wllh. sai da ya
musu haka wajan sau 15 sannan suka ce kai zamu
ci uban ka fa ya zaka raina muna wayyo kaita sako
mu cikin daji. sai daya ya juya baya yaga baya
hango titi balle motar su. yace kan uba. ku duba
baya. suka waiga suma sunyi mama kin nisan
da,sukayo. daya ya falle deeny da mari yace dan
uban ka dama karya kake. deeny yana sheshekar
kuka yace wllh yallabai ba karya nake ba. can
deeny ya daga kai yaga wata garka can makekiya.
yace yallabai wllh kaga garkar can.suka ce lalai ka
raina mana wayoo wajan sau ashirin fa kenan kana
muna haka. amma karka ce mun kware ka da
sharadi. kaga daga nan zuwa garkar can da ka
nuna yanzu da nisa ko. deeny yace haka ne. police
din wanda shine babba a cikin yan sandan yace. to
idan muka je mukaga ba haka bane. wllh ka kuka
da kanka dan wllh sai mun zanee ka kuma kayi
tsallan kwadi tundaga wajan har nan. deeny gaban
shi na faduwa yace naji. na yarda. suka kama
hanya suka nufi garkar deeny kuwa gaban shi sai
faduwa yake yaji irin abunda za'a mishi idan ba
garkar bace. ai kuwa tun daga nesa ya hangi wani
rami irin an cire rogo a wajan ai kuwa ya fara
murna. sukuwa hararan shi kawai suke. suka
karasa bakin ramin. daya ya kalli deeny yace dan
ubanka wannan rogo aka cira a wajan ba ramin da
kace kayi bane. deeny duk da yasan ba shi bane
amma haka ya rike gardama wai wllh shine. deeny
hada hawaye yana tunanin idan aka koma kotu fa
hukuncin kisa za'a yanke mai bayan wahalar da
zasu bashi a nan.
yana cikin tunani. su kuwa har sun aika a ciro
bulala. haba sai ganin wanda aka aika nayi ya dawo
a guje yana fadin kura kura. su kuwa cewa suke
dalla can a wannan dan dajin ya za'a yi a sama
kura. deeny kuwa add'au yake allah yasa kurar ce
ma ya samu ya tsere. suna juyawa kuwa sukaga
wani katan kare kai saika ce kura. karan baki wul
da shi ga gashi kamar buzun kare. suka ce wa
wanda ya rugo yana cewa kura.,banza ashema
kare ne kake cewa kura. bari mu kashe. wannan
dan iskan karan. ai kuwa suka nufi karan da
kulakan su da nufi suci uban shi. shi kuwa karan ko
matsawa baiyi ba. daya yaje maka ma karan kulki
kawai sai gani sukayi ya bace bat. ai kuwa ido ya
raina fata. shima deeny da yake gefe yana kallo
abun ya bashi tsoro dan saida ya razana. suka
duba sama ko kasa basuga karan ba. ashe wannan
karan mai gonar ne ya tsafa su sunkai su 20 irin su
ashe dayan tafiya yayi ya kirawo sauran. ai kuwa.
suna tsaye sai ji sukayi wata irin guguwa ta tashi
sama……………https://m.facebook.com/groups/1232550283531628












→BANI NA KASHE TABA← PART 16
N@ BIGBOY isah
> suna tsaye suka ga irin karnu kan nan sai
zubowa kasa suke yi. ai kuwa da yan sanda da
deeny duk suka ari ta kare. sai gudu. su kuwa duk
karan da ya fado kasa sai ya nufe su da gudun
bala'i haka sukai ta tsere a cikin daji gudu kuwa
har sunyi sun fara gajiya daga sun waiga baya sai
suga wannan karnuka na biye da su da gudu.sunkai
mint 30 suna wannan mugun gudu. daba na wasa
ba gudun cetan rai sunsan in har suka bari
karnukan nan suka kamo su baza su bar ko da
kashin su ba. ai kuwa suka hango wani makeken
gida. auka nufe shi kuwa suna zuwa suka tura
kofar gidan suka ci sa'a ta bude su duka hudun
suka afka ciki suka rufo kofar. su basuyi tunanin ko
gidan waye bama a cikin dokar daji haka. su officer
anji jiki. duk sun yarda hulonan su a cikin gudun
nan nasu. kowa ya zauna sai haki suke sai huci. to
da suka huta ne fa suka ce ku tashi mu tafi suka
tashi ai Wannan dan iskan yaran duk shi yaja wo mana wannan bala'i ai tashi sukayi daya ya kama get din da niyar ya bude ai kuwa ina gamgam take ko motsi bata yi ogan cikin su yace me ke faruwa akace kofa taki buduwa yace baku da hankali gyara nan ya kama get din da kansa yaja yaja  kuwa kofa taki buduwa abun ya basu
mamaki sukayi sukayi kofar taki buduwa. ido kuwa
ya raina fata duk sukayi zuro zuro su basu karasa
cikin gidan ba kuma kofa taki budewa. haka suka
ce ta fanjama fanjam suka nufi cikin gidan duk su
hudun yanzu kowa ta kanshi yake ba maganar sa
deeny tsakiya.shi kuwa deeny ba haka ya so ba so
yayi ya tsere tun kafin su shigo gidan. to sai dai
daga ya juya sai yaga kare ya kusan kama mai
kafa. da yaga dai ba wajan tsira shi isa ya biye
musu har suka shiga gidan<
>
acan lagos kuwa aliyu ne ya nema Transfer da
yake shima police ne. a cewar shi gwara ya koma
gida kano zai fijin dadi. ai kuwa aka bashi Transfer
hada hutu ya samu na 1month. ya taho gida kano
da murnar shi. su maman deeny ne a tsakar gida
da ita da amina matar kawu kenan duk su biyun
sunyi jagwam jagwam suna ta tunani gobe idan aka
sama matsala za'a yanke wa deeny hukuncin kisa
fa. Idan ba'a gaskata zancan saba. sai sukaji sallama da sauri amina ta daga kai da
yake tasan mai wannan muryar aliyu suka ga ya
shigo ai kuwa murna duk suka amsa slm suka
tarye shi sai farin ciki suke sun ma manta da
damuwar da suke ciki..
Ni wllh alhj duk jikina yayi sanyi da jin zancan yaran
nan wllh gani nake kamar ba zai iya kashe halima
ba. maman halima ce ta fadi haka. wai ke wace iri
ce toh kin san manufar sa ne kika san ko dama can
ba santa yake ba so yake ya sace zuciyar ta daga
nan sai ya kaita yayi kudi da ita ko ai mazan yanzu
basu da gaskiya duk yan yau darane. ni kuwa nace
har kai ko. yaci gaba da cewa ai ba'a gane mugu
daga fuska ko daga dabi'arsa. ita dai maman
halima bata yarda deeny ya kashe halima ba. Domin tasan irin shakuwar dake tsakanin su har
zata kara magana sai ya daga mata hannun yace
dakata dan allah. kawai ya tashi ya shige dakin sa.
wayar hajiya ta dau kara. tana dubawa taga maman
Yazeed  ne. ta dauka suka yi gaishe gaishan su. nan
maman yazeed take cewa maman halima. gasu nan
zuwa.…………… https://m.facebook.com/groups/1232550283531628


mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group
bigboy
on-line 23.04 13:57
→BANI NA KASHE TABA ← PART 17
@N BIGBOY isah
tace gamu nan zamu zo dama shima yazeed din yana
da dan aiki da,zai yi a kano din. wannan karan har
da abban shi zamu zo. ko dan jin maganar
.maman halima tayi murna sosai da jin wannan
maganar. tatashi cikin farin ciki ta nufi dakin alhj ta
fada mai shima yaji dadi sosai. sbd ya dade bai
gana da yayan nashi ba. haka ranar akai ta girke
girke da soye soye. da yake shida
dan nasa kudi har sunyi musu yawa zance amma
duk kudin yazeed alhj bai san inda yake samo su ba
yasan dai albashin yazeed bai ko kama kafar kudin
da yazeed din ke facaka da su ba. alhj ya tambaye
shi ya tambaya har ya gaji amma saidai ya cemai
wai kudin salary sa ne da kuma busines da yake
dan juyawa da ita.amma alhj bai yarda ba sbd
kudin ba na wasa bane kuma lokaci daya kudin
akaga sun shigo masa. suna abuja amma a sati
sau biyu yake kwana a gida. idan suka ce ina yaje
sai yace wai harkar Businesses dinsu ne duka ya
koma kano. Misalin karfe hudun yanma anata jiran su maman yazeed amma shiru su alhj sanusi ne da matar sa zaune a parllo suna jiran zuwan su alhj bashir. Ko lfy har ynz basu karaso ba ai yaci ace sun karasa ynz kafin ta rufe baki wayan alhj yayi ring ya dauka alhj bashir ne yace mai suyi hkr baza su sama zuwaba sbd wani aiki da ya taso mai..<
>acan kuwa su anne ne suka fito sukaje wajan
maman anne. maryam ta gaida ta.ina ta amsa tana
zolayar maryam.wai yau ta kwana a bukka.
maryam tayi murmushi. anne tace mama ina abun
karin su gwaggon mu tafi maryam ta raka ni mu kai
musu. maman anne tace toh gashi ku kai musu
kuyi sauri ku dawo kuma kuzo ku karya. koko da
kosai ne sai tuwo. wai sune wayayu a garin shine
kokon aka zuba shi a cikin wani tshohn jog ne ja.
cike da koko. sai kosai a wata kula. towo da miya a
langa babba da karama. anne ce ta riko kwanan
tuwan da miya maryam kuwa ta dau koko da kusa.
suka fito suka kama hanyar gidan gwaggo suna
tafiya suna hira kamar dama can kawaye ne. fulani
kuwa sai kallan su ake ga anne da bakuwa yar
bunni. anne kuwa sai bude baki take. tana kallan
mutane tana dariya.ita kuwa maryam gaban ta sai
faduwa yake ta rasa dalili har sai da ta fadawa
anne. anne tace kodai gamuwa da yayan nawa ne
ya jawo haka kin san fa yayana kyakyawa ne.
maryam murmushi kawai tayi. a zuciyar ta tace
haba wa a kauyan nan har akwai wani saurayi da
zan so. suka dai ci gaba da tafiya anne sai zuba
surutu take.
gwaggo ce ta zauna kusa da halima tana cewa ya
jikin halima tace wllh da sauki sosai wai ni kuwa
har yanzu fa banga jikan naki ba gwaggo. gwaggo
tace ai yanzu zaki ganshi kin san yana wajan
farauta ne.assalamu alaikum. sukaji ance. suka
amsa. halima kuwa dayar muryar taji kamar ta
maryam amma da tayi tunanin me zai kawo
maryam nan sai kawai ta basar tace ba ita bace.
sai ji sukayi ance tsohuwa fito ga kokon ki. kina ina
ko dai kin mutu ne. anne ce tace haka. gwaggo
daga daki tace ai bazan mutu ba sai kin mutu ynz
yara suke fara mutuwa. sannan ne anne ta isa
kofar dakin tayi salm ta shiga ita kuwa maryam a
waje ta tsaya da kofin koko a hannun ta. yanda taji
gaban ta sai kara faduwa yake da ta matsa kusa da
dakin. anne ta kalli halima da itama kallan ta take
tace. gwaggo bakuwar yar burni mukayi halan.
gwaggo tace ke sai kin nuna kauyan cin naki a ko
ina ko. anne tace hb tsohuwa ai nima ga kawata
yar birni. ta mika hannu daya baya wai ta kamo
maryam sai taji bata nan.da sauri ta juya maryam
maryma. sai ta sama maryam a kofar daki
tsaye.anne tace haba maryam kamar dai ke ma
yar fulani ce. zomu shiga mana. kawo kokon.……… https://m.facebook.com/groups/1232550283531628


08096831009









→BANI NA KASHE TABA← PART 18
@N BIGBOY isah
tana shiga dakin tayi tsaye tana kallan halima.
itama halimar kasa yin motsi tayi ta kurawa
maryan ido itama. anne da gwaggo su kuwa duk
sun saki baki ganin kallo kallo da ake tsakanin
maryam da halima. gwaggo ce tace lafiya ko kun
san juna ne. sannan ne maryam ta gane ashe suma
su anne suna ganim halima da ta dauka ita kadai ke
ganin ta. maryma tace halima wai kece anan me ya
kawo.ki nan. halimar ma cewa tayi maryam me
kika zo yi nan. maryam ta karasa kusada halima ta
zauna a kan gadan da halimar take sannan
tace.aunty nayi mamakin ganin ki anan. halima
tace hmm kedai bari allah ne yayi da sauran
rayuwata ai. nidai tun lokacin da muna tare da dina
ya tafi sallah ya barni a mota. ni kuma ina nan a
mota nayi zuru zuru sai raba ido nake gani a bakin
titi mutane kuma duk an shiga sallah shima deeny
tuni yayi alwala ya kabara sallah. basai ganin mota
nayi an parka ta a kusa da ni ba wasu karti na gani
sun fito da sauri daya ya bude lid din motar dayan
kuma ya dauko wani pillow ga duk kan alamo dai
cikin wannan pillown akwai guba. cikin hanzari tayi
shirin fita ta dayan kofar kawai sai mutum ta gani a
tsaye da pillow a hannun sa kafin tayi yin.kurin iho
tune ya hada mata baki da hanci ya danne da pillow
dayan kuma ya ririke hannun ta kuma ya danne
mata kafafu saboda shure shuren da take can
sukaji ta yi lakwai bata iya motsi baban naku mugu
sai cewa yayi kai kumurci saketa mana bakaga ta
mutu ba ko gawar ma kashe ta zakayi.dai dai nan
suka kula anyi zaman tahiya a masallaci za'a salam
ce ne da sauri suka kukule kofofin motar suka ruga
da gudu tasu shi kuma ogan nasu yana ciki yana
jiran su aikuwa suna shiga yaja mota . nidai tun
daga lokacin ban farka ba sai a nan gidan. gwaggo
da anne duk sun tausaya mata. suna tunanin to
waye yazo binne ki tace nima dai ban sani ba itama
maryam tayi jum kadan sannan itama ta kwashe lbr
ta duk ta gaya musu sukayi mamaki sosai.
sallam sukaji anyi duk suka amsa. halima kallan
saurayin take azuciyar ta tace wannan da alamo
shine wanda ya cetoni. ita kuwa maryam kanta a
kasa ta kasa dagowa ta kalle shi ma. sakamakwan
gaban ta da taji yana faduwa. cewa yayi gwaggo
ina kwana ya jikin bakuwar gwaggo ta amsa. tace
bakuwa gatanan har ma ta warware har hira muke.
anne ce ta durkusa tace yaya isah ina kwana.yace
lafiya lau ya mamana. maryam jin anne tace yaya
da sauri ta daga kai tana kallan sa taga ita yake
kallo shima. ai kuwa a tare suka kauda
kai.sakamakon wani mumunan faduwar gaba da
sukaji su biyu. wai me hakan ke nufi daga kallan
yarinya gabana ya fadi. nida naga yan mata kala
kala. iri iri. duk ina kura musu ido amma ban taba
jin irin haka ba sai yau isah ne ke fadar hk a
zuciyar shi. maryam kanta a kasa tace ina kwana
yaya isah ya dan kalle ta sannan yace lafiya kalau
yace sis wannan fa ya tambaya annee. annee tace
wannan sunan ta maryam jiya muka hadu da ita
yan daba sun biyo ta allah ya kawo ta garin mu a
dandali muka hadu kuma a gidan mu ta kwana.
bayan anyi shiru daga can halima tace yaya ina
kwana ya amsa lfy ya karfin jikin tace jiki da sauki.
yace to allah ya bada sauki amma baki bani lbr
abunda ya faru da ke ba. halima ta kwashe lbr kaff
ta fada mai. ya girgiza kai alamon mamaki. sannan
kuma anne ta ci gaba da bawa yayanta lbr maryam
sai da ta fada mai duk tun daga fitowar maryam
daga gida har zuwa sace ta da tserowar da tayi da
haduwar su duk ta fada mai komai yayi jum kadan
can sai yayi wupp! yace mutum nawa kika ce ya
kalli halima tace uku.ya juya kan maryam yace
kema uku ko. maryam da kanta ke a kasa ta dago
ta kalle shi da kwala kwalan idanon ta masu daukar
hankali tacje eh su uku ne. ..........   Washhh har naji dadi halima bata mutu ba kufa ???? ."










→BANI NA KASHE TABA←




Part 19



N@  bigboy isa






Yace tabbas mutum daya ne yasa ayi muku wannan aiki domin kuwa la'akari da labarin ko wacce daga cikin ku amma  ba wani wanda kukawa laifi kuwa ko wulakan ci ko maka mancin hk duk suka girgiza kai alamun babu yace to alhmdulilah ynz dai tunda allah ya tsalllakar daku ku biyun yanzu abunda yafi shine zamu jira kudan huta kafin mu tatara mu tafi birni can wajan iyayan ku domin kuwa bamu san wane hali suke ciki ba a halin yanzu. Duk wannan zancan da yake yanayi yana satar kallan maryam lokacin nema ya dan gaskata zcyar sa a bisa zargin da yake akan maryam. Gwaggo tace gaskiya ne allah ya maka albarka sannan yace gwaggo ni zan fita ya mike hade da kallan wajan da Maryam ke zaune ai kuwa kamar hadin baki suka hada ido wani zazafan faduwar gaba sukaji a tare cikin su kowane ya rasa daliln haka.nan dai ya fita ya barsu sai hira suke shi kuma ya nufi gidan su wato gidan su anne domin haka yake duk safiya sai yaje ya gaishe da iyayan sa ( hmm iyaye ba abun wasa bane ya kamata mu lura mu kyautata musu wani zaka same shi shi gani yake gaida iyayan sa ma kamar wani zubar da class ne alhalin kuma wannan dabi'ar banza ce bata kirki ba allah yasa mu gane ameen) yaje yayi sallama aka amsa ya kuwa iske su a daki suna hira ya tube takalmi ya shiga dakin ya ce ina kwanan ku suka amsa ya gwaggo inji maman anne yace duk suna lafiya wllh baban yace kaga munyi bakuwa ko eh baba nima dama ina so in gaya muku jiya bayan  na fita farauta da dadare sai na biya ta garka to kaiwai sai naga mutum yana rami na dauka barayi ne kawai sai na far masa na bisa ina harbi amna allah bai bani saa na same shi ba ya shiga motanshi ya gudu to ina dawowa wajan kuma sai na iske mutun ashe wai mutum yazo binne wa dana taba kawai sai naga macece lokacin kuma anyi sa'a ashe wai dogwan suma tayi kuma lokacin da naje ta farfado kawai sai na dauke ta na kaita gida ynz dai tana can ta farfado  ta sama sauki sosai sudai kawai gyada mai kai suke jin abun sukayi kamar al'mara  badan mgnr daga bakinsa take fitowa bama da wanine ke fada musu cewa zasuyi karya ne. yaci gaba da cewa umma kuma wani abun  mamakin shine da yarinyar da ta zo nan gidan da kuma wacce na tsinta sun san juna wai kawaye ne ma  maman anne ta rike baki tace sarautar allah kenan shine yayi ikon sa a kansu. sannan tace to ai yanzu kamata yayi muje can gidan gwaggonka domin asan mafita domin kuwa iyayansu zasu shiga wani hali. baban anne yace to kuyi gaba nima  gani nan zuwa ynz ba irin tashi hankali da kuma fargaba da maman deeny ta shiga ganin har an kwana kuma ba labarin su deeny har yanzu basu dawo ba domin sai zarya take police. su ma haka yan gidan su halima ya daya kenan ita kadai gare ta yanzu idan ta mutu ya zatayi gashi yanzu na daima haihuwa hawaye ne zafafa suka  kwaranyo a idanonta can kuma sai naga ta tashi ta bude wardrobe ta dauko hijab  tasa ta fito ta ko ina zata oho haka ta fita rai a bace ko ta kan driver bata bi ba domin gani take bata lokaci ne ta fito haka mai gadi ma ko kallo bai isheta ba balle ma ta fada mai inda zata napep naga ta tsaida..... ..........      


big boy kune










  😫🔫  BANI NA KASHE TABA  😫🔫




Na 👑 king boy👑



Part 20






Tana tsayawa ta shiga tace muje nan baya zaka kaini ranta a murtuke… bata zame ko ina ba sai kofar gidan su kawun deeny wato dai wajan mamar deeny ta zo. Tafito ta nufi cikin gidan ganin bata da niyar bashi kudin sa ne yace hjy kudin fa. Jirani haka tace mai ba tare da ta juyo bama. Suna zaune Suna zaune suna jimami sai ji sukayi. Murya kamar daga sama ku fiddo min ya'ta tana hawaye dan allah ku taimaka min ku bani yarinya ta ita kadai na mallaka sai hawaye suka fara zarya gaba daya hankalin su ya tashi bama kamar maman deeny tace ga kujerq zauna mana aa ba zama nazo yi ba nidai kawai ku taimaka min ku fiddo min da di'yata mamar deeny kasa cewa komai tayi daga haka kawai kuka take abubuwa sun mata yawa ko abinci kwanan nan biyu bata iya ci duk ta rame. Aliyu naga ya fito daga dakin sa wanda yana jin duk abunda ke faruwa yazo gaban maman halima ya kalli maman deeny yace wannan ita ce mahaifiyar yarinyar? Kai kawai ta iya daga mai alamun eh ya maida hankalin sa ga matar wacce kuka yaci karfin ta sai sharar hawaye take da hijab dinta ya yi kasa da murya sannan yace inaso ki kwantar da hankalin ki ki saurari abunda zan gaya miki pls ki natsu ya dauko wata kujera ta katako wa ajiye sannan yace zauna ba gardama ta zauna ita da farko da niyar masifa taxo amma harga allah yanda ta iske su suma gidan gaba daya ba wani walwala shi yasa taji duk jikinta yayi sanyi. aliyu yace to da farko inaso ki natsu kiyi tunani sannan zan gaya miki wannan maganganun ne bawai dan baki sani ba aa kawai dan tunatarwa yace ki san cewa komai mukaddari ne daga allah duk abunda ya faru da mutum to daga gare sane alkhari ko makaman cin sa saidai abunda wasun mu basu gane ba shine a lokacin da allah ya sauko da alkhairi ga mutum sai yay ta jin dadi wani ma baya godewa allah domin gani yake kamar wayansa ne ya kawo mai wannan alherin. gaba daya maman deeny da maman halima da kuma ita kanta amina wato maman sa duk sunyi shiru shi kawai suke sauraro. yace to idan kuma allah ya jarabci mutum da wata masifar kuma sai mutu kaga duk ya rikice a nan ne ma zai tuna da allah hmm shi kuma allah zaima wannan abun ne dan ya gwada iya imanin ka..... nandai yata mata nasiha itadai tayi shiru sauraran  sa kawai take.yace to ina so ki dauki wannan abun a matsayin kaddara sannan ki dage da addu'a domin addu'a itace maka min mumuni yace ke naki mai sauki ne ma domin ke kin fara cire rai ga yarki domin ance ta mutu ya nuna maman deeny yace kinga maman  sa nan itama da shi din da kuma maryam wato kanwarsa duk ba daya daga ciki domin ita maryam tun ranar da abun ya faru ta tafi islamiya bata dawo ba har yau shi ma dini kuma haka domin suma basu dawo ba daga binciken da suka tafi  mamar deeny wasu zafafan hawayan ne suka kubuto mata wanda ita kanta hjy khadija wato mamar halima saida ta tausaya mata sannane ma ta san wai maryam bata dawo ba yace ynz abunda za'ayi shine kiyi hakuri ki koma gida kici gaba da addu'a domin lamarin nan sai addu'a dai. jiki ba kwari ta tashi ta musu salama duk a kunyace domin yanda ta shigo musu da fari tana fita da tarar da dan adaidai tar nan inda ta barsa ya fiddo waya sai chat yake abunsa shi kam yama manta da wata yake jira chat yayi dadi ta hau tace mayar dani inda ka dauko ni. yayi mamaki shima yanda yaga matar da farko cike da damuwa ynz kuma gashi ta fito ba kmr dazu ba ya tuka ya maida ita tana sauka bata tsaya tambyar ko nawa ne kudin ba ta zaro 1000 sabuwa dall ta mika mai domin tasan kudin sa baikai hk ba ta wuce zata shiga gida yace hajiya chanjin fa tace ka rike ba tare da ta waiwayo ba dadi ne ya cika shi shi kuma domin riba biyu ga ya huta kuma ga kudin da ko lokacin aiki yake bai isa ace dubu ta shigo ba yaja adaidaitar sa yayi gaba tana shiga gidan sai  wayarta tadau kara tana dubawa taga hjy saratu ce take kira ta dauka suka gaisa nan take tmbyar ya lbrn halima tace abundai gashinan sai addu'a nan hjj saratu take gaya mata suyi hkr da basu sama zuwa ba amma ga yazeed nan zuwa yau yau....  ...........




A CAN BANGARAN SU DEENY KUWA.........






ISAHN ♥ KUNE








  😫🔫  BANI NA KASHE TABA  😫🔫




Na 👑 king boy👑



Part 21


.

CIKIN gidan suka nufa suna waige waige yana yin gidan ya fara furgita su domin ko motsin basuji ba wata kofa ce katuwa wacce akayi da zinary a sukazo kofar dakin sukayi curus kowa yaki yarda ya fara taba kofar ogan ya kalli deeny da jikin sa ke rawa yace kai zo ka bude mana kofar nan dan uban ka. Haka ya taho yana makyarkyata kamar ya kama kamar kuma yaki saidai yasan ba yanda ya iya
Wata zuciyar tace mai kai koma fa kun kubuta daga gidan nan to ba makawa kashe ka za'a yi domin banda wannan hujar ba wata tunda anzo ba'aga ko ramin ba kaga kuwa ba makawa kashe ka za'ayi sai yaji duk tsoro ma ya fita a ranshi. Ya rufe ido yayi yan addu'o'i sannan ya sa hannu biyu ya tura kofar  da yake kofar mai hannu biyu ce kamar get gani sukayi kofar ta bude kai tsaye Suka nufin parllo suka fara salama shiru basuji ko motsi ba hakan yasa suka kutsa kai sukayi cikn. Katan farllo ne tan gameme yasha ado kujeru ne jere birjik a parllan ga kuma can wasu dakuna ba adadi a jere sai kalle kalle sukeyi domin dakin ya hadu sosai durum wuta sukaga ta dauke hade da wata shu'umar dariya hahahaha muna maraba da ku yau abinci har gida hhhhhhh dadai zuwa mukeyi mu kamo da karfin mu ko musa sihirin mu mu kama amma yau muna maraba da sauyin da yaxo mana cikin wannan masarauta hahahahaa kuma sai sukaji tsik dariyar ta dauke wuta kuma ta dawo a kame na gansu waje daya ko wanne cikin su sai karkarwa yake deeny kuwa da yake baya wasa da addu'a tun da yaga wannan al'amari ya dukufa karanta →ayyatul kursiyu← ( yan uwa mu bar wasa da addu'a duk a binda kaga zai firgita ka saka allah a ranka ka fara addu'a zakaga dace sannan tsoranka zai fita allah kasa mu dace ameen) can kuma sai hasken ya fara ya kawo ya dauke can kuma sai gaba daya dakin ya zama ja jawur wata kofa sukaga ta bude wasu karti ne ke futuwa daga ka gansu kasan ba imani ko kadan a ransu gasu bakake duk ba riga sai Ja jayan wandu na a jikin su da kuma jan kyalle a kansu sun dadaura.kowa ta kansa yayi dukan su kofa suka nufa da gudun su kowa na ta kansa wutar dakin ta dauke dub..   can jimawa kadan sai wutar dakin ta kawo kowa ganin sa yayi a hannun kato guda hankalin su tashe kowa sai fizge fizge yake deeny ne kawai baya fizge fizge kasan cewar shi tuni ya sadaukar da rayuwar sa a zuciyar sa kuwa addu'a  kawai yake wani tsoho ne ya fito kanaa duk furfura cikin fararan kaya idanunsa jawur da  alamun dai shine shugaba a wannan gidan  hahahaja haka ya taho yana dariyar mugunta yaxo gaban su daya bayan daya yana kare musu kallo sai fizge fizge suke deeny kadai ya gani a nutse yaje gaban sa ya tsuguna tsayin su yazo daidai yace yaro nan fa gidan mutuwa ne nan gidan shan jini a ci nama ne nan gidan a tarihin sa ba wani mahaluki da yake shigowa ya fita da rai in ba dan kungiya ba amma kai me yasa naga kamar baka damu ba alhalin kasan mutuwa zakayi
deeny ya dago kai wanda har lokacin gabansa faduwa kawai yake da ya hada ido da mutumin nan duk sai yaji tsoro ya fita a jikin sa ya samu kwarin gwewa. yace hmmm me kake tunani ne da kake fadar wannan mgnr ko dan banyi mamaki ba domin kai ba imani a zuciyarka bana tunanin kana da ilimin sanin allah da har zakasan shine mai kashewa mai rayawa ba kuba. hakika maganar deeny ta bata masa rai. ya daka masa tsawa kai yaro ni kake gayawa wannan bakaken maganganun ya kama habar deeny ya zaro wata wuka ya dora mai a wuya yace sake fada mgn daya in baka sheqa lahara ynz ba kuma jinin ka zamu sadaukar da shi ga gunkin mu sanan namanka yan kungiya ne zasu cinye hahahahah mgnr da deeny ya fada itace ta tsaida shi daga dariyar hade da jin wani mugun bacin rai kamar xuciyar sa zata kone. kai jahiki ne wannan mgnr ce ta fito daga bakin deeny wanda har ynz wukar ce a wuyansa. can kuma sai ya tuntsire da dariya hahahah i like this boie ina san marar tsoro irinka da zaka shigo kungiya mu da ka huta yaro da ka more dadin duniya kuma kaci arziki ka barsa hatta jikokin ka ma bazasu yi talauci ba. tirr tirr da wannan muguwar kungiya taku da zaka gane alherin lahira shine yafi dacewa da ka nema jindadin duniya aikin banxa ne....... waya tayi ringing wani kato ya mikowa ogan wayar sir bad boy calling ya amsa wayar ya kara a kunne yana kallan deeny hello bad boy daga can kuma hw ar u dady 5yn dad i will come 2 kano 2day wow am hppy  bad son kafin kazo kuwa zan tana dar maka baban abun tarya. tnx dad bye. ok bad. tashi yayi daga wajan deeny yake fadawa wannan kartan bad boy na hanya dan haka dole a tanadar masa muhimmin abu ya kalli yan sanda wanda duk a tsure suke yace waye oga a cikin ku waye babba? kowa ya nuna dan uwansa ogan ma na gefan sa ya nuna suka kama bararabi. tsawa ya daka musu nace waye babba yana karkarwa ya daga hannu yallabai nine ku kawo min shi nan. saida akazo gaban deeny dashi sannan yasa wasu kartai suka danne wannan ogan yan sandan yasa wuka wuluk sai ga kai a kasa............ king boyn kune










😫🔫 BANI NA KASHE TABA 😫🔫.




  Na big boy isah



Part 22






Gaba daya sauran yan sanda sun kidime sakamakwan basu saba ganin kisa irin wanan ba deeny kuwa ido ya lumshe hade da cewa ya allah. Ya daga kai sama. Hahahahaha tshon ya fara dariya suma kartin nan gaba daya sai suka kama dariya can kuma sai yayi shiru kamar hadin baki suma kuma duk sai sukayi tsit sannan ya nuna wasu karti hudu yace ku dauki wannan naman ya nuna ogan yan sandan nan kuje ku gyarama oga domin yana nan tafe cikin yan secondna tuni sun dauke sa ya dubi su deeny yace  kuma duk waka zamu muku domin ba mai shiga gidan nan ya kubuta kuma baza'a fara a kanku ba dan haka sai ku shirya yana gama maganar ya juya ya nufi wani dakin har zai shiga ya juyo ya kalli wani kato daga cikin kartan nan yace ku kaisu dakin ajiya ya juya ya shige dakin .....



su anne ne zaune gidan inna sai tadi suke su ukun kmar dama kawaye ne gwaggo tace ai gwara ku tashi ku tafi can gidan ku ta kalli anne tunda kinga yamma tayi anne kuwa cijewa tayi wai ai ita bata so a rabasu da halima duk dadai tare da maryam zasu koma tace inna me xai hana mu kwana a nan ynz inje in kawo mana abincin rana da dadare ma haka inje in kawo ina tace to kwantar da hankalin ki tare da halimar zaku tafi can ku kwana uwar iyayi har zaki fara kawo mana kabli da ba'a di  ba yanzu kuka sha fura ba har wani abinci rana kuma za'a ci da sauri su maryam suka kalli kaka. kaka fura ce abinci rana kuma cewar maryam. kaka ta rike baki ohh ni ya'su  yanzu bayan furar nan  har wani abinci kuma za'aci. anney tace hmm kunga ku kyale ta ai tsohuwa ce ita ta kusan margayawa shi yasa bata iya cin abinci da yawa amma ko ni nan ai cikina ba komai nake jinsa. su duka suka hau dariya halima tace ai ni fura dan marmari kawai nake shanta ba dan koshi ba. kaka tace kundai hade baki ko to ai sai ku tashi ku tafi can gidan kuci abinci ni dai na koshi furar na ta ishe ni har gobe da safe duk suka zaro ido gobe fa. Anne ce ta tashi oya standup following me tayi gaba su kuwa dariya sukayi turancin yar rugga....

tafiya suke su kunya suke ji duk jikin su ko gyale babu duk ba wacce ke da gyali a gunta ga mutane sai kallan su ake ita kuwa anney sai wani bun kasa take ita wai with yan bunni haka sukata tafiya duk garin ba mai kyau anney saka makwan gata fara da kyan diri hadee fuskar ta yar doguwa ma daidai ciya duk da yake ba duguwq bace sosai amma kuma ba gajera ce ba duk da su maryam yan burni ne basu saba da wahala ba ba abunda zasu nunawa anney saidai ma ta nuna musu da yake yar fulani ce
Tafiya suke suna ta shiririta sun biye wa anne ta saya musu wannan ta saya musu wannan sai washe baki take tana tare da yan bunni. A haka har suka karasa suka iske maman anne tuni ta dafa abinci su kawai take jira da yake tanada yar sauran shinkafa itace ta idasa dafewa suka shigo da salamar su ko wacce da murmushi a fuskarta haka anne taje ta dauko musu tabarma roba wai a cewar tayan burnine ba tabar mar kaba za'a basu ba. Suka zauna a ka zubo musu a tran silva suna ci suna hira salama sukaji. Gabaki daya suka amsa hade da kallan kofar shigowa  da sauri maryam ta kauda kai ganin mai salamar ba wani bane isah ne rike da zoman daji dayan hannunshi kuwa ya riko kwari da gwafan shi...................oooppppps




King ne ♥










BANI NA KASHE TABA 😫🔫.




  Na big boy isah



Part 23












Maman anney ta fito da mamaki a fuskarta dannan sannanka da zuwa yau kuma kane a gida da rana haka abunda bakayi.ya sunkuyar da kai wanda ya kara bayana kyan fuskar sa tare da cewa uhm uhm..... Yama rasa me zaice ya kama in ina gaba daya suka kama kallan sa maryam ce kawai taki dagowa domin in suka hada ido wani abu take ji na daban da ta rasa minene. Cansai yace ummana dama wannan na kawo muku ya daga xomo tare da nunashi.tace hmm dama kana kawo mana xomo a haka ne ai sanin da nayi saika babake ka gyara kake kawo mana

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *