Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, June 17, 2019

TASNEEM complete littattafan hausa novel

adsense here
TASNEEM complete littattafan hausa novel

TASNEEM complete littattafan hausa novel

[8/23, 7:05 PM]

     💥💥TASNEEM💥💥


Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
                N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*1 to 5*

Hadari ne Sosai a Garin Gangara dake jahar Katsina, Garin Ya Murtuke yayi baki sosai sai iska da akeyi ba kakautawa, Duk wanda Kagani a hanya Sauri yake wasu Sassarfa, Wasu kuwa Har gudu suke Saboda kada Ruwan ya tarar dasu ahanya, Daga gafe na hango wata Yar Yarinya Fara Sol wacce bata Wuce Shekara Goma Xuwa sha daya bah, Hannunta Rike da Roba Wacce ake kira da Hanji waje, Ciki da Ragowar Xogale da kuli, Tafiyanta take hankalinta kwance tana Yan wakokinta, Sam bata damu da Hadarin dake Garin bah, Ban Ankara bah naji An fara Yayafi Mutane Sai gudu Suke Wasu nasamun Mafaka Saboda kada Ruwan ya tabasu, Itako yar yarinyan nan Tafiyanta take bata damu da yayafin da ake bah, Ban ankara bah naji ruwa ya tsinke gaba daya, Leman dake hannuna na bude na cigaba da bin yarinyan nan, Abin mamaki sai naga ta aje roban hannunta Ta tsaya cikin Ruwan sae Tsalle take tana Dariya ita kadai, Wata tsawa akai wanda hakan yasa Ta dauki robanta dasauri ta sunduma a guje, Niko *summy Abduol* Binta na cigaba dayi har bakin wani shago danaga anan itama ta rakube, Daga Ciki naji ana Cewa "ke tasneem Wallahi bakya jin magana" ta juya ta kalleshi tareda bata fuska tace "tho me kuma nayi yaya?" Ya hade rai yace kinga ruwa maimakon kisamu inda zai fake shine kika taho haka koh? Salan mura ya kamaki kisani zuwa chemis dinda ban shirya bah, Ta turo baki tace tofah ba wajan fakewa neh, Girgiza kai kawai yayi baice komai bah..

Ruwa ake sosai kamat da bakin kwarya, Cikin shagon ta shige ta rakube tanata zazzare ido, Chan ta dago tace yaya, Ya juyo yace menene?? Tace in dauka?? Ta buna biscuit, Yace Aa, Tadan yi narai narai da ido tace dan Allah yaya, Yace Tasneem kinsan Fah bah shago nah bneh na Baba Ado ne, Kuma kinga fa duk kayan nan nashi neh, Tace to inje in tambayeshi? Yace Aa ya dauka ya mika mata sannan yasa Hannu a aljihu ya ciro naira biyar yasa A kwalin da suke aje kudi..

Murmushi tai tace nagode yaya, baice komai bah ya cigaba dasauraran radion shi, Saida ruwan ya tsagaita sannan tashiga gida ta chanza kaya ta dau roban xogalen ta nufi gidan Goggo, ta Shiga da sallama, Goggo ta amsa ta fito tace harfa gabana ya fadi na dauka ruwa ya miki duka neh, Tadanyi dariya ta aje roban ta mika mata cinikin tace Ya tabani anma bah sosai bah, Goggo ta zaro ido tace ikon Allah, Allah dai yasa kar kiyi mura in shiga uku, Tasneem batace komai bah ta mike tadau tsintsiya tace Goggo duk gidan naki yayi dati barin miki shara, Goggo tai murmushi tace kai anmafah nagode..

Tas Tasneem ta share gidan taima Goggo wanke wanke Sannan Taima Goggo sallama ta nufi gida, lokacin har anFara kiraye kirayen Sallan magriba, Gida daya ne a tsakanin su dan haka bata dau lokaci bah takai gida lokacin Taga Tasiu na rufe shago, Tace yaya masallaci zaka? Kai ya gyada mata Sannan yace maza ki shiga gida, tace tho ta shiga gida dasauri, Iya ta gani tana kwashe tuwo ta karasa tace Sannu iya, Harara ta wurga mata dan haka sum sum tabar Tsakar gidan ta shiga dakinsu...
Sai da akai isha Sannan Tasiu ya Shigo dakin, Tasneem na Kwance kan tsohuwar katifan ta tai Lamo, Tasiu ya hade rai yace kinyi sallah?? Girgiza kai tai ya kallam mata harara yace maz tashi kiyi sallah, Mikewa tai zaune Sannan ta kalleshi tace Ya tasiu Yunwa nakeji fah banci komai bah, Yadnyi shiru Sannan yace Ba'a baki abinci bah?? Ta girgiza kai dasauri, Mikewa yayi cikeda damuwa yace ina zuwa kamin in dawo ki tabbatar kinyi Sallah, Tho tace tareda mikewa Shikuma ya fita, Salame ta samu a tsakiyar gidan ta fiti wanke hannu yarinya Iya wacce take Sa'arta, Salame tace Tasneem baki zo dakinmu wasa bah, Tasneem tace Iya tace na daina zuwa kema ai kinga korana take, Salame tace kinci abinci?? Ta girgiza kai, Shiru tai sannan tace tho zan Yanko miki idan iya ta zaga, Tho Tasneem tace tayi alwala ta koma dakinsu, Aiko chan Saiga Salame da tuwo ta turo ma tasneem cikin daki ta koma dasauri..

Rabi Tasneem taci ta aje ma Yayanta Rabi dukda bata koshi bah, Chan Su gashi yayi Sallama, Tasneem ta amsa, Ya shigo hannunshi da plate am rufe da leda, ya aje Sannan yace ga indomie kici, Tace Lah! Yaya ga salame ta kawomin tuwo har na ajema Sauran, murmushi yayi yace tho kici indomie din barin ci Tuwon, Tace tho ta dauka taci kadan ta turamai sauran Ya Ci Sannan Suka danyi hira ya koma Shago..

Washe Gari da Sassafe ta tashi ta Share dakinsu kamar yanda taga Salame nayi, Sannan ta shirya cikin kayan makarntan ta na LEA duk da sun tsufa da kuma kode anma kayan sun mata kyau sosai, Jakanta ta dauka na buhu ta fito ta nufi dakinsu salame gabanta na faduwa, Muryan Baba ado taji a dakin, Hakan ya bata daman shiga da Sallama, Baba ado yace Tasneem har an shiryo?? Tai murmushi tace eh baba ina kwana, Yace lapia lau, Ina fata iya ta baki abinci kinyi kari?? Satan Kallan iyan tai tako ga ta wurgo mata harara Sannan tace eh baba, yace to madallah Adawo lapia, Ya kwallawa Sallame kira ta fito, Sunma Ya tasiu Sallama Wanda ke cikin shago yanata saida kaya Sannan suka tafi, A hanya Salame ta fito ma Tasneen da koko da kosai Data diban mata a leda, Tasneem tai godiya Ta samu guri ta zauna Taci Sannan suka karasa makaranta....

Ummu Farheen✌🏻
   




[10/15, 6:51 AM] ‪+234 813 184 5457‬: [8/26, 11:49 AM]

       💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
               N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*6 to 10*

Suna dawowa ta shiga gidan Goggo, Goggo cikeda Fara'a ta zauna tace Sannu Goggo, Goggo tace Yauwa Tun dazu nake jiranki kizo ki ci danwake, Tasneem ta washe baki tace tho Goggo, Zama tai goggo ta kawo mata Ta baje ta soma ci, Rabi taci ta mike, Goggo tace ina zaki?? Tasneem tace zan kaima Ya tasiu neh nasan baici abinci bah, goggo tai murmushi tace cinye saina Samai kikai mai, Tace tho ta koma ta zauna saida ta cinye Sannan Tadau na Ya tasiu ta kai mai...

Yana zaune bakin shago shida Abokinshi,  ta karaso, Ta gaida Su Sannan ta aje tace Ya Tasiu na tafi kaima Goggo zogale kasuwa, Ya tasiu yace tho karki dade sannan kinsan gobe za'a koma islamiya, tace tho, Wani paper tagani a hannun Ya tasiu tace Yaya Wannan takardan pah?? Hararanta yayi yace tho Sarkin tambaya Ina ruwanki, Turo baki tai tabar wajan tana gungunai...

Ta koma gidan Goggo tadau roban tai mata Sallama Sannan Ta dau hanya, Har tayi nisa Ta hango wani gidan gona Wanda kullum in zata wuce Sai taga Ananta Fitowa da Buhuhuna, Tabe baki tai tace Yaudai Sai naga menene a Wannan gidan, Bakin gate din ta tsaya tana Leke, Fruits ta gani iri iri ana Sakawa a buhu ana dinke bakin, Hadiye miyau tai ta shiga cikin gidan da sanda, Wani ta gani Sanye da malun Malun Fari kar ya bata Baya, A hankali tace Mallan dan Allah kace su bani guda daya, Juyowa yayi dasauri dan ta matukar bashi tsoro, Dattijo ne wanda Zai kai kaman shekara Sittin, Hannunshi Rike da sanda Sannan Fuskanshi Sanye da Medicated Glass, (```Madubi mai kara karfin ido```) Gabanshi ne ya fadi, Ya kura mata ido kur! Tace Baba Dan Allah kace su bani wanchan..

Juyawa yayi ya kalli abinda take nunawa, Apple ya gani Yayi Murmushi yace Tanko kawo ma yarinyan nan, Tanko jiki na rawa yace tho Alhaji, Apple kusan Guda Hudu ya mika mata, Murmushi tai dimple dinta ya lotsa tace Alhaji nagode, Murmushi yayi yace Ya sunanki?? Tace Tasneem, Shiru Yayi ya kura mata ido gabanshi na cigaba da faduwa, Kallanta ya cigaba da yi Lallai yarinyan nan namai matukar kama da wani ko wata Anma sam ya manta inda yasan fuskar, Katse mai tunani tai dacewa Alhaji! Ya juyo yana goge gumin Fuskar shi yace Na'am, Tace nima ka daukeni aiki a nan in rinka zuwa inacin Wannan "ta nuna mai Apple din hannunta" Dariya yadanyi kasa kasa yace au! Ashe Cinyewa zaki rinka yi bah Aiki bah, Tai murmushi ta cigaba da cin Apple dinta...

Saida ta cinye guda biyu tas Sannan ta kalli Alhaji tace nah tafi Zanje kasuwa na saida ma goggo zogalen ta, Sai a Sannan yaga roban dake gabanta, Yace Tho nima kawo zan siya, tace na nawa?? Murmushi yayi yarinyan tana burgeshi, Santa da kuma tausayinta suka shigeshi yace Zuba min kawai Sai kisa ma su Tanko, Tace tho! Ta zuba mai sannan kowa tasa mai Bata ankara bah taga zogalen ya kare...

Ta zaro ido tace Lah! Alhaji xogalen ya kare kuma baka biya bah, Yace nawa neh kudin?? Tace na dari biyar ne, Murmushi yayi ya dauko yan dari dari sababi guda biyar ya mika mata, Da fara'a ta amsa tace Dama ance duk Mai suna Alhaji mai kudi ne, Dariya yayi yace inji wa?? Tace haka ya Tasiu yace, Ta yatsine fuska sannan tace Anma Alhajin layin islamiyan mu bashida kudi kullum sai mutane sunzo Amsar bashin su, dariya yayi sosai, Ta Zauna kusa dashi tace Alhaji?? Yace na'am tace Ance duk wanda aka cemai Alhaji yaje Makka, Kaima Kaje???

Ummu Farheen✌🏻
             N
Aysha Gana💕
[10/15, 6:59 AM] ‪+234 813 184 5457‬: [8/27, 7:24PM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
              N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*11 to 15*

Dariya Alhaji yayi Sosai Sannan Yace "Tasneem knan Naje Makka sau Hudu" Zaro ido tai tareda rike haba Tace "Tabdi! Alhajin Layin Islamiyan mu koh Bai taba zuwa bah" Alhaji Yayi Murmushi Yace "Tho Zaije shima indai Allah ya kirashi", Gyada Kai tai kawai, Tadau Robanta Tace "Alhaji na tafi gida Kaga Har Yamma tayi kuma Idan na Dade Ya Tasiu Zaimin Fada, Yace Tho, "Gobe ma Zakizo??" Kai ta gyada Mai yayi Murmushi Yace "tho ki gaida Ummanki", To kawai tace Tabar wajan dasauri, Tambaya ne Fal a Cikinta Har ta isa gida, Shagon baba ado a rufe dan Haka ta shiga gidan Goggo, Ta mika mata kudin, A rude Goggo ta kalleta tace "na shiga uku ni Fati Tasneem!"

Tasneem ta kalleta tareda Yamutse Fuska tace "Na'am menene duk kika rude?" Goggo cikeda tashin hankali tace "ina kika samu wayan nan sabin kudin?? Ina fata bah Juye aka miki bah?" Tasneem tai Murmushi taba Goggo labarin Alhaji harda Apple dinda Ya bata, Ta nuna ma Goggo Sauran Tace na Ya tasiu neh, Murmushi goggo tai tace yar Gidan Tasiu, Tasneem ta mike tace "na tafi goggo kada Iya tamin Fada, Goggo tace tho shiknan saida safe"

A Tsakar gidan taci karo da Salame, Tace "Tasneem yanzu baba yace naje dama na duboki" Murmushi tasneem tai tace "ai ina gidan goggo tun dazu" Baba ado daya fito dan Yin Alwala yace "Yaki nan Tasneem" ta karasa Ta gaida shi ya amsa Sannan yace "Tho yaudai Yima Goggo talla ya kare tunda gobe za'a koma makaranta", Tadab turo baki sannan tace "Tho Baba" Yace "Maza aje ai Sallah Magriba tayi" Kamar ta tambayeshi Sai kuma ta share tadau Buta Ta dibi Ruwa tai Sallah, Tana Idarwa Ta nufi Shagon Ya Tasiu, Ta Gaidashi Sannan ta nemi Guri ta zauna, Saida Ya gama Abinda yake sannan Yace "Tasneem ya Akai??" Tai murmushi tareda Mika mai Apple din hannunta, Cikeda Mamaki yace "Aina kika samo wannan tasneem??" Zama tai tabashi labarin duk yanda sukai da Alhaji, Ajiyan zuciya Tasiu yayi yace "Banaso ki kara zuwa Wajan" Tai narai narai da ido tace "Saboda meh Ya Tasiu?" "Kawai" yace a takaice, Shiru tai tana Share kwalla, Ya kauda da kai dan Sam baisan Ganin kukanta, Ganin Kukan Bana Kare bane yasa Ya janyota..

Saida Ya Lallasheta tai shiru Sannan Tace "yaya!" Yace "Na'am Tasneem" Tace "Yaya Dama Ana zuwa makka sau hudu??" Yace "Eh mana indai mutum nada kudi zaije har fiye da haka" Tai Shiru sannan Tace "Tho Yaya Mamanmu Ta taba zuwa??" Yace "meyasa kika tambaya Tasneem?" Tace "tho bakace Babanmu nada kudi bah??" Shiru yayi kamar bazai amsa bah chan kuma ya kalleta yace "Ta taba zuwa Hajji harda Umrah" Murmushi tai tace " Tho mu Ya Tasiu Yaushe Zamu??" Yace "Nifa Surutun ki ke hadani dake" Turo baki tai tace "Shiknan Zan fadama Alhaji ya Kaini tunda kai bazaka bah" Ya zaro ido yace "oh! Danace kar ki kara zuwa wajan Alhajin bakiji bah koh?" Ta Turo baki Batace komai bah, Yace "In gani koh inji Labari Wallahi saina Tattaka ki" Narai Narai tai da Ido batace komai bah, Ganin Yana kokarin rufe shagon yasa ta tashi Ta fita ya rufe a tare suka shiga cikin gidan, Hayaniya Sukaji na tashi daga dakin iya, iya Tace "Mallam Tsintarciyar mage fah bata mage, Banga dalilin dazai sa kace dole sai nayi abinci naba yaran nan bah" Mallan ya kara Harzuka Yace "Dole ki basu, Sai dai idan Bakison zaman gidan nan lapia" "Keh Barin gaya miki akan tasneem da Tasiu wallahi zan iya Sakinki Ki koma gidanku" Dasauri Tasiu yaja Tasneem zuwa dakinsu, Jikin tasiu Yayi Sanyi Sam Baiso yaji iyayen rikon Nasu na fada akansu, Tasneem Tace Ya tasiu muma mu koma gidan mu Arinka bamu abinci Kamar yanda akeba Salame da Shatu, Baice komai bah ya mike..

Salame ne Tai Sallama A dakin, Langan Da ake sama mallan Abinci ta dire agaban su Tace "Gashi inji Mallan" Cikeda Mamaki Tasiu Yace "Kice Mun Gode" ta Kalli Tasneem tace "Gobe ki shirya Da wuri zamu islamiya" Gyada Kai Tasneem Tai Salame ta fita, Haka Suka Ci Abincin Tasiu nata Sake Saken Abin yi Saboda zaman Gidan, Saida sukai Sallan Isha Sannan Suka Kwanta, Barci Gagaran Tasiu Yayi, Duk Sanda ya tuna Da Mahaifan su sai hankalinshi Ya tashi, Dakyar ya samu Barci ya daukeshi goshin Asuba...

Ummu Farheen✌🏻
           N
Aysha Gana💕
[10/15, 7:05 AM] ‪+234 813 184 5457‬: [8/29, 5:31PM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
            N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*16 to 20*

Latin Tashi Yayi Har Saida Tasneem Ta tasheshi, Alwala yayi ya nufi masallaci, Tasneem ta mike knan Zata fito dan Yin Sallah Iya ta shigo dakin a fusace, A Tsorace Tasneem Ta mike, Iya tai mata Wani irin Kallo Sannan tace "Ina Yayanki?" A tsorace Tace "Yaje Masallaci bai dawo bah", Shatu ta banko kofa ta shigo, Tsaki tai Tana Kallan Tasneem tace "Maiya Kawai Ni iya kinsan Abinda ke damuna??" Iya ta girgiza kai Shatu tace "Yarinyan nan duk inda kika bi indai ana Lissafin masu kyau itace ta farko, Yarinya Sai kyau kamar Mayya" Iya Ta doka tsaki tace "inaso na bar Miki Sallau idan Yayanki ya dawo ki fadamai Kada in kara ganinshi a Shagon Mallan" Shatu ta rike kugu Sannan tace "Sannan ke Tasneem duk abinda Za'ayi a gidan nan kezaki rinka yin shi, Ta rike Kunnen Tasneem tace ina fata kinji??" Gyada kai Tasneem tai tana Hawaye, Shatu ta kara Murde ma Tasneem kunne Sannan suka Fita..

Zama Tasneem tai Ta Baza kuka, Kuka take Sosai, Tunawa Datai Idan Ya tasiu yadawo Batai Sallah bah Zai ci mata Yasa Ta mike Ta fito, Bakin Rijiya Taci Karo da shatu tana Fito da kwanonin Wanke Wanke, Tai Tsaki Sannan tace Kina Idar Da Sallah ki fito kiyi wanke wanken nan, Sannan ki Share Gida, Sannan ki tabbata Kinje tuka tuka kin dibo ruwa kin Cika mana Banbu, Kai Tasneem ta gyada dan tasan Halin Shatu tsap Zata mata duka, Dasauri tai alwala ta shiga daki Tana cigaba da kuka, Saida gari yadan Waye Sannan tasiu ya Shigo gidan..

Zaune ya sameta kan Sallaya Tana Rusa kuka, Zama yayi dasauri kusa da ita yace "Lapia Tasneem meyafaru kike kuka??" Kara Rushewa da kuka tai Ya Kura mata ido nadan Mintina, Yace "Fadamin mana Menene??" A hankali Tace Ya Tasiu Ka kaini gurin mamana ni banaso na zauna Anan, Shiru yayi baice komai bah, Ganin kukan bana kare baneh Yasa Ya Shiga lallashinta, Dakyar tayi Shiru Ya mike ya Nufi Shago...

Shatu na ganin ya fita ta leko tace oya Tashi muje, Bah musu Tasneem ta mike Tabi bayan Shatu, Tsaye Tama Tasneem dole Sai ta wanke kwanukan, Salame ta fito daga dakinsu Tace "Lah Shatu Tasneem Fa bata iya Wanke Wanke bah ki kawo ni inyi," Hararanta Shatu tayi sannan tace "Bar nan wajan Ko ki Sani", Salame Ta hade rai tace "Allah Shatu idan Baki kyale Tasneem bah yanzu zanje na Fadama baba", Shatu najin Haka tabar Wajan dasauri ta nufi dakin iya..

Salame ta kalli Tasneem tace kyaleta kawo ni nayi, Tare da Tasneem din Sukai Wanke wanken, Iya ta fito a Fusace Tace "Lalla Salame, Albasa dai batai halin Ruwa bah Wallahi", Salame ta turo baki tace "meh nayi??" Iya Ta galla mata Harara tace "Ban sani bah, Tho Wallahi bari kiji duk randa na kara saka tasneem aiki a gidan nan kika hana saina hadaki keda ita na zane", Zaro ido Salame tai tace "Iya bakyau fah A islamiya mallamin mu yace Kaji tausayin Wanda bashida mama da baba" Iya ta kara Galla mata Harara tace "tho uwata Yimin Wa'axi, In banda ke doluwace Yarinyan nan ta hana kinsamu Soyaiyar mahaifinki" Jin Muryan mallan Yasa Sukai Shiru Tasneem ta koma dakinsu Dasauri..

Bakwai nayi ta shiga dakin Mallan Har kasa Ta durkusa ta gaida Shi ya Amsa Fuska a Sake, Yace kin karya?? Kai ta gyada Alamar Aa!, Iya ya kwalawa Kira ta shigo tace gani, Kallanta yayi cikeda Mamaki Yace "Ina Abin karin Tasneem??" Tsaki tadanyi sannan tace yana Daki taje ta dauka, Ya kalli Tasneem yace je kidau na Tasiu kikai mai Sannan ki dau naki, Tho tace Ta mike Ta Nufi dakin...

Saida ta shasha Dunguri da zagi gurin Shatu da Iya Sannan Suka barta ta dauka Ta kaima Tasiu Sannan Tadau nata, Tana Gamawa Ta Shirya cikin Kayan islamiyan tah, A Tsakar Gida Sukaci karo da Salame Suka Wuce...

Suna Dawowa Tasneem ta kalli Salame tace lah! Salame na manta pencil dina a aji, Salame tace "Tap bazan jiraki bah Ni na tafi, Kije ki dauko", Murmushi Tasneem tai tace tho Sannan Ta Koma dasauri, Gidan Gona Ta nufi, Tana zuwa Alhaji na zuwa, Kyalkyalewa da dariya tai tana kallanshi Har Yayi parking motarshi, Ta karasa dasauri tace Alhaji nima Zaka koyamin mota??

Ummu Farheen✌🏻
            N
Aysha Gana💕
[10/15, 7:09 AM] ‪+234 813 184 5457‬: [8/30, 5:44AM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
            N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*21 to 25*

Murmushi Yayi Yace "Tasneem bah Gaisuwa??" Tadan yi Dariya tace au! Ina kwana? "Lapia lau" yace Sannan Yace "Ya gida Ya Ummanki da Abbanki?" Shiru tai idonta ya kawo kwalla, Alhaji Hankalinshi ya tashi yace "Tasneem menene?" Tace "Ni bansan Ummana Da Babana bah" Alhaji ya girgiza kai cikeda tausaya wah yace "Sun Rasu neh??" Ta kara Girgiza kai Alamar Aa!, "Tho ina suke?" Cewar Alhaji, Tasneem ta gyara Zama tace "Nima ban sani bah, Kullum idan na tambayi ya Tasiu Sai yayi Shiru ko kuma ya Fara kuka" Shiru Alhaji yayi Cikeda tunani, Katseshi tai dacewa "Na tambayi Baba Ado shima yace Yasan Su, Shima idan nace aina Suke Sai Yayi Shiru" Ta kalli Alhaji tace "Alhaji tho kai kasan su??" Girgiza kai yayi Alamar Aa...

Hawayen dake makalle a Idonta Suka zubo, Tace "Ni banason Gidan Mallan Kullum Sai Shatu tamin fada Kota Dungureni", Alhaji ya juyo da Dubanshi Gareta Yace "Wanene Mallan??" Tace "a gidan muke Ya tasiu namai Tsaron Shago" Shiru Yayi Zuciyarshi na Raya Mai Kila Iyayensu Duk sun rasu neh Ba'aso a fada mata, Wata Zuciyar Tace Yarinyan Nan Jininka Ce!, Dam! Gabanshi ya fadi, Zufa ne ya karyo mai, Tasneen tace "Alhaji Yau baka bani Wannan Abin bah" Murmushi yayi ya kira Tanko Aka Kawo mata...

Hira takemai Sosai duk da Rabi shirme neh, Ta mike dasauri kamar Wacce Aka Tsikara, Alhaji Yace "Ina zaki?, A rude Ganin Rana ta fito tace "Gida xani daga Islamiya nake" Alhaji Yace "Tho Gobe Zaki Dawo??" Gyada Kai Tayi, Hannu Yasa A Aljihu Ya ciro Sababin Hamsin Guda Goma yace "Gashi kiyi Anfani  dasu duk randa Iya bata baki abinci bah" Zaro ido tai ta matsa dasauri tace "Bah ruwana Ya tasiu zaimin duka" Ganin bazata amsa bah yasa Ya mata Sallama Ta kama Hanya Tana Sauri, Binta Yayi da Kallo cikeda Tausaya Wah, A Ranshi yana Kwadayin Taimaka Mata Itada Yayanta...

Gida ta dosa gabanta na faduwa, Tasan yau Bah abinda Zai hana Ya Tasiu dukanta, Ta Maza Tai ta karasa Kofar gidan, Ajiyan zuciya tadan Sauke Ganin Shagon A rufe, Tunawa datai kila yana Cikin gida Yasa Cikinta ya Kada, Dakyar Ta Yunkura ta shiga gidan, Salame ta gani a tsakar gida tana Wasa da Yar Tsanan ta, Salame tace "Tasneem sai yanzu kika dawo" Gyada kai tai Tana Zufa, Karasawa Tai kusada Salamen tace "Ya Tasiu na Daki koh?" Salame ta girgiza kai tace "tunda na dawo ban ganshi bah" Ajiyan Zuciya Tasneem ta Shiga dakinsu, Kaya ta Chanza Sannan ta Fito ta zauna kusada Salame Suka cigaba da wasa da Yar Tsanan Wai Suna mata Kitso...

Har Akai azahar Tasiu bai dawo bah, Hankalin Tasneem ya Fara Tashi, Gidan Goggo ta Shiga Taga Itama bata Nan, Ta fito tadawo gida, Salame ta kawo mata Abincin Ranan Ta Tace "Tasneem zo muci", Girgiza Kai Tai Tace "Ni bazanci bah Sai ya tasiu ya Dawo" Salame tace Kila fah babane Ya aikeshi, kuka Tasneem ta Fashe Dashi, Bata Kara Rudewa bah sai dataga anyi La'asar Shiru Bashi, bakin Shago ta zauna tanata Kuka tana kiran sunanshi A Hankali, Salame ta fito sanye da kayan Makarntan Islamiya Tace "Tasneem tashi muje" Tasneem ta juya tareda rungume hannu Ta Noke Kafada, Salame tace Zai dawo nasan fita yayi, Tasneen ta Cigaba da kukanta ta Juya baya, Muryan tasiu Sukaji a kansu Yana "lapia ke bazaki islamiyan bah" Jiyowa tai dasauri ta Rungume shi, Ya Kalli Salame Yace Lapia? Salame Ta Fadamai komai, Yayi Murmushi yace yi hakuri Naje Jarabawa neh, Ta kalleshi cikeda mamali tace Jarabawan meh?? Yace jamb, Baba ado yabiya min, Murmushi tai yace Maza jeki Shirya kizo ku wuce, Ta koma ta shirya Ya bata Naira hamsin yace ta siya wani abu taci tunda bataci komai bah, Ta amsa tai godiya suka Wuce...

Ummu Farheen✌🏻
           N
Aysha Gana💕
[10/15, 7:11 AM] ‪+234 813 184 5457‬: [8/30, 3:31PM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
            N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*26 to 30*

Haka Rayuwa Ta Cigaba Da wakana a Gidan, Kullum Tasneem tana Fuskantar Wulakanci da Tsangwama gurin Shatu da Iya, Kullum Salame ke kawoma Tasneem abincinta Suci tare, Shakuwa Sosai ta Shiga tsakanin Alhaji da Tasneem, Jinta Yake kamar yarshi, Duk Sanda Ya mata kyauta Bata Amsa Saboda Tsoron Ya tasiu...

        *********

Tasneem ce Kwance Kan tsohuwar Katifan Tah Bayan ta idar da Sallan Asuba, Tasiu ya Shigo da Sallama Ta amsa Ya xauna Kusada Ita, Ta Mike ta Zauna, Hannunta Ya kama Saiga Hawaye Sharr, Ta Kalleshi Cikeda Mamaki Tace Ya Tasiu Bah kyau Babba na kuka fah, Hannu tasa Tana goge mai Hawayen, Dakyar Ya iya Cewa, "Banaso na Rabu dake Tasneem, Bansan Halin Da zaki shiga bah rashi nah" ta Kalleshi da mamaki tace Yaya Ina Zaka?? Ya dukar dakai yace "Mallan Ya samo min makaranta A Zaria Abu, Zan Tafi Yau" Ta kalleshi Idonta Ya ciko da kwalla, Tace "Yaya"

Dagowa Yayi ya Kalleta Ta Fashe da kuka Tace ni Yaya Tare Zamu, Zan Bika, Shima Kukan yake Yace "Dah Zai yuwu Tasneem da mun tafi tare" Anma Bazai yuwu bah, Ta kara Fashewa da kuka Tace ni Dai mu tafi Tare bazan Zauna Bah, Ganin Dagaske take yasa Ya Shiga lallashinta Yana Bata Baki..

Kuka take sosai Haka Shima, A haka Ya hada Kayanshi, Shirun da Mallan Yaji ne yasa Ya leka dakin, Zaune ya samesu sun hada kai Sai kuka Suke, Mallan ya shiga dakin Ya kamo Hannun Tasneem da Tasiu yace Ku Yayana Neh Tasiu, Karka damu Zan Rike Tasneen Amana, Insha Allah bah abinda zai sameta, Share Hawaye Tasiu Yayi Ya kalli Mallan Yace Nagode Baba, Bah abinda Zance dakai sai godiya ka daukemu kaman Yayanka, Nagode baba...

Mallan Ya dafa Tasiu Yace karka damu Tasiu, Allah yana Tare dakai, Kuka Tasneem ta kara Fashewa dashi ta rungume Tasiu tace "Dan Allah yaya Karka tafi ka barni" Mallan Sai Lallashin Tasneem yake anka Ta Kekyashe Taki shiru, Haka suka rabu Tasiu kuka Tasneem kuka, Sallame Itama tana Taya Tasneem, Shatu ko murna take dan Tasamu abinda takeso, Ynzu zata Samu daman Cin Uban tasneem Yanda Takeso, Haka Tasneem na Rungume Tasiu Tana Ihu, Dakyar Mallan ya banbareta daga jikinshi ya kaita gidan Goggo sannan Ya Tasa Tasiu Suka tafi...

Ko A gidan Goggon Kuka take Sosai Tana kiran yaya tasiu, Goggo Sai bata Baki Take, Dakyar ta Samu tai Shiru barci ya kwasheta, Haka Tasneem ta yini Sukuku Daga kuka Sai kuka, Bah Yanda goggo batai da ita taci abinci bah anma Taki, Sai Kuka datake, Kan Kace meh Zazzabi mai zafi ya Rufeta...

Hankalin Goggo bah karamin tashi yayi bah, Mayafi ta yafa ta shiga Gidan Mallan, Iya ta samu bakin murhu Tana iza wuta, kauda kai tai gefe Sannan tace ina wuni goggo, Goggo tace Lapia ina Ado?? Tsaki tadanja kadan Sannan Tace baya nan Tunda suka fita da Tasiu, Goggo bata kara cewa komai bah tabar gidan, Chemist ta nufa ta hado ma Tasneem Magunguna Sannan Ta dawo, Koda Ta dawo barci ya dauke Tasneem Duk da rawar Sanyin Datake...

Ummu Farheen✌🏻
            N
Aysha Gana💕
[10/15, 7:27 AM] ‪+234 813 184 5457‬: [8/31, 7:58AM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
            N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*31 to 35*

Yanda Aka gaya mata anasha Goggo ta baballa, Ta dibo ruwa. A hankali ta shiga tashinta, Tasneen ta bude ido dakyar tace "Ya Tasiu ka dawo neh?? Dan Allah karka tafi ka barni" goggo ta tayar da ita zaune ta bata Maganin Dakyar Tasha Sannan Ta kwanta...

Alhaji Shiru Shiru Yau Baiga Tasneem bah, Hankalinshi duk ya tashi gashi yau tamai alkawarin Zata kaishi yaga yayanta Tasiu, Ganin Shiru Shiru yayi yawa yasa Ya Kira Tanko, Yazo dasauri yadan duka Yace Gani Alhaji, Alhaji yace "Dan Allah Tanko ko kasan Gidan su Yarinyan nan datake zuwa nan?" Tanko ya girgiza Kai dasauri Sannan yace "Aa Alhaji ban sani bah", Kai Alhaji ya gyada yace "Tashi kaje, Tanko ya mike Yabar wajan, Haka Alhaji Ya yini A Wajan baiga Tasneem bah, Jikinshi a Sanyaye Yabar Gidan Gonan Ya nufi Gida...

Kwana Biyu kenan da Tafiyar Tasiu, Tasneem ta koma gidan Goggo, Har Yanzu taki daina kuka, Tun Goggo na lallashinta har Abin Ya fara bata Haushi, Kullum Sai ta fito ta zauna bakin Shagon Mallan wanda tun bayan tafiyan tasiu yake a rufe Taita Kuka tana kiran sunanshi, Sallame ke kokarin Shigowa Gidan Tana Janta da wasa ko Zata warsake anma ina!..

A kwana biyu duk Tasneem ta Rame Saboda Rashin cin Abinci, Daga kuka sai kuka sai anbatan Sunan Tasiu, Saida mallan ya mata jan ido Sannan ta dan soma cin abinci, goggo da kanta take wanke mata kaya Ta kaimata Ruwan wanka, Wani lokacin goggo dakanta take mata wankan...A haka har Tayi Sati daya, Dole Mallan ya Sata Take zuwa makaranta, Wani lokaci dakanshi yake zuwa Ya kaita makarantan Itada Salame...

Kullum sai Alhaji yazo Yakan tambayi su tanko ko tasneem Tazo, Anma Kullum Maganan Daya neh "Batazo bah" Wani lokaci Dakanshi yakan dan zazzaga ko Allah zaisa yaganta, Anma Bah ko Alamanta...

Yau Ranan Sati Salame ta biya ma Tasneem islamiya, Zaune ta sameta a dakin Goggo tayi tagumi tasa Koko da kosai agabanta, Hawaye kawai ze zuba a idonta, Salame ta karasa Ta zauna kusada ita tace "Tasneem kiyi hakuri Ai mallan yace Ya tasiu zai dawo idan sun samu hutu, kinga Yace idan Kika daina damuwa wai zai kaimu birni idan zashi kasuwa" Tasneem ta dago tana murmushi tace Dagaske?? Gyada kai salame tai Sannan tace "Ki karya mu tafi" Kokon Tadansha kadan ta mike Tasa kaya, Har sun fito daga dakin, goggo ta fito daga ban daki Tace "Islamiyan za'a??" Salame ne tace "Eh goggo ina kwana", "Lapia lau" Keh Tasneem ina fata kin Sha kokon nan" Eh kawai tace Goggo tace tho Adawo lapia, Ameen Salame tace suka fita...

Ko a Islamiyan Tasneem Hankalinta baya Kan Karatun, Tunanin Ya Tasiu Kawai take har aka tashi, Suna Hanyan Dawowa Salame Tace "Tasneem Iya Ta aikeni bakin Kasuwa ko zaki Rakani??" Girgiza kai Tasneem tai Salame tace "Tho sai na dawo" Sannan tadau hanyan kasuwa, Tasneen tafiya take a hankali kanta na Kasa, Kamar ance Alhaji ya Fiti daga mota ya ganta, Kira ya kwalla mata ta juya A hankali, A Sanyaye ta Karasa kusada shi Ya Kalleta cikeda kulawa yace "Tasneem Lapia Bana Ganinki Kusan sati biyu knan"

Kallanshi tai Idonta Ya ciko da kwalla Yace Fadamin menene?? Ta fashe da kuka tareda langwabar dakai Sannan tace Ya tasiu Ya yafi ya barni, Zaunar da ita yayi Sannan Yace kamar yaya ya tafi ya barki?? Ta kara Rushewa da kuka tace "Mallan ya samo mai makaranta Ya tafi ya barni beje dani bah" Dan Murmushi Alhaji yayi yace Ai ba'a Zuwa da wani Tasneem, Karatu fa zashi, Ta Dago jajayen idonta ta kalleshi Tace "Iya da shatu dukana zasu rinka yi tunda benan"

Ummu Farheen✌🏻
            N
Aysha Gana💕
[10/15, 7:30 AM] ‪+234 813 184 5457‬: [9/1, 5:50PM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
            N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*36 to 40*

Alhaji yace "Saboda meh?" Kuka ta cigaba dayi batace komai bah, Lallashinta Ya shiga Yi Har tai Shiru Sannan Yace "Tho Yanzu Wajan Wah kike?" Tace "Goggo" wacece Goggo Alhaji ya tambaya Tace "Kakansu Salame neh" Shiru Yayi na Wasu lokuta Zuciyarshi na Suya Sannan Yace "Tho Kina Zuwa Makaranta?" Kai ta gyda Yace "Wani Aji kike??" Tace "Primary Five"..

Iyyeh Kice Babbar Yarinya ce, Dan Murmushi Tasneen tai, Alhaji yasa Aka kawo mata mutumin ta Apple Tai godiya Sannan Ta kalli Alhaji Tace "Alhaji!" Yace "Na'am Tasneem" Ta kara Murmushi Sannan Tace "Ina neh Gidanka??" Yayi yar Dariya yace "kinaso kije neh??" Kai Ta gyada Sannan tace Banaso Nazauna Gidansu Salame, Yayi Shiru Yana Kallanta Yace "Kinaso ki koma gida nah?" Tace eh mana Bah kace zaka koyamin mota ba kuma kace zaka kaini Makka, Murmushi yayi yace "Sosai kuwa insha Allah Tasneem, Mikewa Tai Ta doka Tsalle tana dariya, Shima dariyan Yayi, Ta kalleshi tace Anma Idan Zan koma gidanka harda Ya tasiu da Salame da goggo koh? Kai ya gyada kawai Yana Mata murmushi...

Tace Alhaji Kai meye Sunan Yarinyan kah?? Dariya yayi Sosai, Surutun Tasneem na burgeshi, Shiyasa Duk sanda yake tareda ita Yake Cikin Farin ciki da Annasuwa, Yace Ni banida Yarinya Sai yaro, Ta Bata fuska Tace "ni Bazanje Gidanka bah", Ya gwalo ido yace Saboda meh Tasneem?? Tace Ni Yarinya nakeso sai mu rinka ma Yar tsana Kitso tare nida ita da salame, Yadanyi Murmushi yace "Tho Sai Insa A nemo miki wacce zakuyi tare" Tace To menene Sunan Yaranka? Yace *Faizan* Kyalkyalewa da dariya Tasneem tai tace "Muko Bamuda Wannan Sunan a Kauyen mu Wai *Haizeen* Ta kuma kwashewa da Dariya, Shima dariyan Alhaji yayi Bah Haizeen bai Faizan, Tace "Oho Wannan Sunan na yan gayu, Ta mike tace Na Tafi Kada Goggo tamin fada, Kudi Ya ciro Rafan Yan naira biyar Ya mika mata, Noke kafada tai Tace "Bah ruwana bazan Amsa bah" Yace Haba tasneem Idan baki amsa Bah Raina zai baci, Hannu tasa ta karba tace nagode Sannan ta ruga a guje tai Gida...

Mallan Tagani Ya Fito daga gidan goggo dasauri, Tace Sannu baba, Ya kalleta Yace ina kika Shiga Tasneem Tun dazu Ga Goggo Batada lapia, Bai jira mai zatace bah yabar wajan, Mamaki ne ya cika Tasneem dazu dazu fa tabar Goggo lapia lau, Shiga gidan tai asauri ta leka dakin, kwance ta Samu goggo tana nishi dakyar, Ta shiga dasauri Ta Zauna kusada ita tace "Goggi bakida lapia neh?" Kai Goggo ta gyada dakyar, Mallan ne yayi sallama Ya Shigo, Ya kalli tasneem dake hawaye yace Jeki chan Gidan tukunna, Tho tace ta mike Ta bar dakin..

Shatu ta samu Tsakar gida, Aiko ta balla mata harara, Dasauri Tasneem tabar wajan ta shiga dakinsu, Bata tara da komai a dakin bah har sudaden katifan ta babu, Zama tai a kasa tana karema Dakin Kallo, Ya tasiu ne ya fado mata a rai, A hankali ta sulale ta gwanta tana kuka ahankali, Sunan Ya tasiu kawai take Fada tana kuka, A Haka Barci ya dauke tah..

Chan cikin barci taji Ana Salati da karfi, Ta tashi dasauri Ta leko, Mallan tagani a tsakar gidan da iya, Abinda taji mallan din na fadi yasa kafafuwanta Suka soma rawa, *Goggo ta cika* Kuka Tasneem Ta fashe Dashi da karfi, Salame tazo kusada ita, Itama kukan take, Tasneem ta kalli Salame cikin kuka Tace "Shiknan na rasa goggo na rasa ya tasiu" kuka suke Sosai,  Dagudu tasneem ta fita ta shiga gidan goggo, Kwance ta sameta an lulubeta da zani, Kara Fashewa da kuka tai ta zauna dabas a wajan, A haka akaima goggo sutura aka kaita gidanta na gaskiya...

Damuwa taima tasneem Yawa dukda karancin shekarunta, Bata aikin komai sai kuka da ambatan Ya Tasiu da goggo, A haka har akai kwana uku, Tun daga ranan rayuwa ta chanza ma Tasneem, Kullum cikin Tsangwama take a gurin shatu da Iya, Kullum sai ta dibo Ruwa Ta share tsakar gida da wanke wanke, Duk ta rame ta lallace Kullum idan Mallan ya tambayeta sai tace ba komai, A haka har Ya Tasiu yayi wata uku da tafiya, Goggo kuwa Wata biyu da rasuwa..

Ummu Farheen✌🏻
        N
Aysha Gana💕
[10/15, 7:34 AM] ‪+234 813 184 5457‬: [9/2, 6:23AM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
             N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*41 to 45*

Yau Juma'a Mallan Ya fito Cikin Sauri zashi Masallaci a kofar gida Yaci karo da Alhaji Sani dake chan Kasan Layin su, Suka Gaisa Alhaji sani yace "Dama Mallan Akwai Maganan Dake tafe dani neh" Mallan Yace "Tho muje Masallaci idan muka dawo sai mu tattauna" Alhaji ya washe baki yace "Tho Bismillah ya nuna mah Mallan tsohuwar abesfan shi" Suka Hau suka tafi Masallaci..

Suna dawowa Mallan Ya Shiga Gida ya dauko musu tabarma, Sun zauna Mallan Yace "ina jinka Alhaji" Alhaji Yayi gyaran Murya yace "Dama game da Yarka ce Tasneem" Mallan Yace "Tho Inaji Ina fata dai lapia?" Murmushi Alhaji Sani Yayi Yace "Mallam Idan Baxaka damu bah inaso a bani aurenta" Kurrri Mallan yayima Alhaji Yana Kallanshi  Sannan Yace "Alhaji ina baka hakuri Tasneem Yarinya ce Shekaranta Sha Daya, Kuma Yarinyan nan amana ce a gurina, Bazai yuwu na zartar da hukunci akanta bah ban nemi shawaran Yayanta bah, Dan Allah kai hakuri, Alhaji ya mike Batare dayace da mallan komai bah yabar wajan Fuuu...

Duk abinda ake Shatu naji Wacce ta boye a xaure tana sauraronsu, Dasauri ta shiga gida tahau kiran Iya! iya!! Kina ina? Iya ta fito tana cewa "Haba shatu wannan wanne irin kira neh", Kurya ta suka shiga Shatu taba iya Labarin duk yanda Mallan sukai da Alhaji Sani, Tsaki ta doka Sannan tace ina mamakin Mallan Wallahi, Gaskiya bazai taba Yuwuwa bah, Kinga Fah idan Alhaji sani ya zama surukin mu zamuji dadi yanda yakeda tarin dukiyan nan, Shatu Tace "Gaskiya neh iya" Anma iya dama ni aka aura mai kinga fa gidanshi gidan hutu ne, Iya ta dungureta tace "Dalla chan Wawiya Inafa hutu, Mutumin da ke dukan matanshi Sannan Ki dora katan Tukunya koh kin manta yaya gareshi" Shatu tace "eh hakaneh" tho yanzu menene abin yi?? Iya tace Zan kirashi ne dan wallahi bazan bar damar nan ta wuce mu bah, Dama mallan zaiyi tafiya Lagos wai zaije Saro kaya, Kinga kamin ya dawo ai shiknan, Shatu ta kyalkyale da dariya tace "ho Iyan mu!"..

Sati biyu da Faruwan Haka da Asusubah Mallan ya tashi dama tun da daddare ya hada kayanshi, Yana dawowa Sallan Asubah Yasamu Tasneem tana Fito da kayan Wanke wanke, Ya kalleta yace "Tasneem meh zakiyi??" Kanta na kasa tace wanke Wanke, A Fusace ya kwalawa Iya kira ta fito tana gungunai, Ta kalleshi tace "Lapia kake kirana da Asubahin nan" Yace "Haba Kina ko jin tsoron Allah??" Na lura tun bayan rasuwan Goggo yarinyan nan duk ta Chanza batada Walwala kuma nasan duk ke kike takura mata" To bari kiji, Yarinyan nan na hana tayi duk wani aiki a gidan nan daga yau" Iya tace Wallahi bazai yuwu bah mallan, Haka yarinya zata zauna bazatai aiki bah, baice komai bah ya shiga dakin ya dauko jakan kayanshi, Ya kalleta yace nidai na fada miki, Sannan idan na dawo naji wani abu tho Wallahi a bakin aurenki...

Kallanshi Tayi da mamaki, Sannan ta tabe baki ta koma daki, Ya kalli Tasneem yace "Allah ya miki Albarka, ki Cigaba da hakuri kinji?" Kai ta gyada Yayi Murmushi yace "meh zan siyo miki?? Tayi Murmushi Har Saida dimple dinta ya lotsa Sannan tace "Yar tsana" Yace shiknan Saina dawo, Adawo lapia Tace ya fita...

Gari na kara Haske Iya ta Yafa Mayafinta ta nufi runfar Alhaji Sani a kasuwa, da Sallam ta shiga ta samu guri ta zauna, Sun gaisa Sannan tace "Mallan ne Ya aiko ni" Yace Wani mallan?? Tace "Mahaifin Tasneem" Hade fuska yayi yace lapia?? Tadanyi murmushi tace "Akan maganan auren Tasneem ne yace Ya amince Sannan baiso ya wuce gobe, Yayi tafiya yau, Yace Liman ne waliyin tah, Alhaji sani ya washe baki yace tho madallah, anma gobe ai yayi wuri, Iya tace bah komai, Koh bakai mata lefe bah babu matsala ka mata a dakinta, Alhaji yace tho Shiknan, Hannu yasa a aljihu ya ciro kudi Dubu Hudu yaba iya yace gashi aci goro, ta amsa dasauri tai godiya tace karka Manta dai Gobe da anyi azahar sai a daura, Alhaji yace tho bah damuwa, Da murna iya ta dawo gida tana ba shatu labari...

Tasneem naji ta fashe da kuka dagudu tazo ta tsugunna gaban iya tace "dan Allah iya kiyi hakuri duk abinda kikeso zan miki wallahi" Tureta Shatu tayi taba cewa Aure kamar anyi an gama yarinya, Kuka tasneen take sosai Tana ba iya hakuri, Salame ce tai Sallama Ta dawo daga Islamiya, Wurgar da jakan hannunta tai Ta karasa kusada tasneem tace menene? Cikin matsanan cin kuka tasneem tace "iya ce zatai min Aure", Salame tace "Aure??" Iya Ta harareta tace "To zoki hana" Fuu Salame ta shige dakinsu, Kuka  tasneem take sosai kamar ranta zai fita...

Iya ko Mayafinta ta yafa Ta nufi makota tana fada musu maganan auren tasneem gobe, Bayan la'asar Wasu datijai Suka kawo kaya, Atamfa guda Uku, Shadda daya, da leshi daya, Sai takalmi daya da sarka, Iya sai murna take, Dubu daya ta basu tukuici Suka tafi, Nan tasneem ta kara tsurewa ta Cigaba da kuka, Har dare kuka take, Zazzabi ne mai zafi ya dauketa wuraren tara na dare, Kuka take sosai a dakinsu tana kiran Sunan mallan da Goggo sai ya tasiu, Iya ta fito a fusace Ta rufeta da duka, Saida tai mata lillis sannan ta turata waje, Duk da ruwan da ake tsugawa...

Rakubewa Tasneem tana cigaba da kuka, Rawar sanyi take Sosai, Dakinsu ta nufa ta dauko Kudin da Alhaji ya bata ta fita daga gidan, Gudu take tana kuka tana cigaba da kiran ya Tasiu, Gidan gonan alhaji ta nufa anma a rufe, Cigaba da gudu tai tana kuka kamar ranta zai fita ga Ruwa da akae tsugawa, Bata ankara bah taji Wata mota na mata horn da karfi, Daburcewa Tayi ta kasa guduwa kan kace meh Motan nan tayi ciki da ita...Innalillahi wa inna ilaihi rajiun...


*This is just the beginning!!!*

Ummu Farheen✌🏻
           N
Aysha Gana💕
[10/15, 7:36 AM] ‪+234 813 184 5457‬: [9/2, 7:56PM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
             N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*46 to 50*

Inna lillahi Wa inna ilaihi Rajiun! Shine Kalmar da na cikin motan ya fada da karfi, Burki ya ci Ya fito Dasauri, Kyakyawan Saurayi ne ya fito daga motan, Wanda A kalla Shekaraun Shi basu wuce Ashirin da Takwas xuwa tara bah, Fatarshi tafi kama da na Black Americans, Gogo ne Bashi da jiki Sosai, Gashin Kanshi luf luf, Sanye Yake da Polo da Jeans Trouser, Hannunshi daure Da i-Watch, Sannan Kafarshi Sanye da Takalmi Jova, Dasauri ya karasa inda Tasneem take kwance cikin Jini, Waige Waige Ya soma Yi ko tareda wani take, Anma baiga kowa bah, Dasauri Ya dauketa Ya Sata a bayan mota Ya shiga Yayi reverse ya Koma...

Gudu yake sosai Yana yi jefi jefi yana juyawa yana kallanta har ya karasa Asibitin, Ko kwakwaran parking beyi bah ya fito, Wani likita ne ya hangoshi Yace Aa! *Dr Naeem* baka tafi bah ko Mantuwa kayi? Kofar motan Na baya ya bude Ya dauko Tasneem Sannan Ya kalleshi Yace "Dr Muje Emergency pls" Dayan doctr Ya Bishi dasauri Suka shiga Shiga Cikin Asibitin, Nurses ne suka amsheta dasauri Amenity Sukai da ita, Dr Naeem ya kalli Dayan Dr Cikeda damuwa Yace "Yanzu ina komawa Na bugeta pls Chck her" Dayan dr ya shiga Ya duduba Tah, Dinki Akaimata a Kafa Har guda biyu Sai Buguwa datai a kai, Likitan ya fito Ya kalli Dr Naeem Yace "Alhamdulillah Bah Wata Matsala baneh sosai" Bayani Yama Dr Naeem, Dan Murmushi Yayi sannan Yace "Thank Uh Dr Sa'ad"...

Dr Sa'ad Yace "Bkmai" Yanzu Sai asamu wanda zai zauna da ita, Dr Naeem Yace "Bakomai Ni zan zauna da ita" Zaro ido Dr Sa'ad Yayi Yace "Haba Dr dakan ka, Ga Nurses sai su Zauna da ita, Girgiza kai Naeem Yayi yace "Babu damuwa Dan ko naje Gida bah abinda zanyi, Shiru Dr Sa'ad Yayi yace "Shiknan Allah Bamu Alheri" Ameen Naeem Yace Ya rakashi Har bakin mota Sannan ya dawo...

Dakin Ya Shiga Da sallama, Kwance Ya Sameta Hannunta Daure da Canular an Sa Mata drip, Sai kafanta Dake liqe da plaster, Kura Mata ido Yayi Yana Kallanta, Kujeran dake Kusada Ita Ya Zauna akai Yana Kara kallanta, Dan Murmushi ya Saki ganin dan Murmushin dake Fuskanta, Wayanshi ne Yadau Ringing, Dasauri ya dauko Daga Cikin Aljihun shi dan baiso Ya tashe tah, Ya Dauka Tareda sallama, Murmushi ya saki Sannan yace "Am fine Mum Ya dad?" Chan Ya kara Cewa Everthing is alryt, Shiru Yayi Sannan Yace "Ok Mum i Will, and my Regrds to Dad" Ok Bye Mum" Ya Kashe ya Kara Maida Dubanshi Ga Tasneem, A hankali Ya furta she's damn Beautiful, Hannunta ya hada da nashi yana Murzawa A hankali, A haka barci Ya Daukeshi...

Har Asubah Tasneem bata Farka bah, Tashi Yayi Yayo Alwala Yayi Sallah, Kamar ance Ya kalleta Yaga Tana Juya kai, Ya mike Dasauri ya Karasa kusada ita Ya rike mata Hannu Sannan Yace "Sannu pls open ur eyes" Magana Yaga Tanayi yasa kunnenshi Dai dai bakinta, "Ya Tasiu" Shi Yaji tana Fada, Ya kara Rike hannunta, A hankali Take Bude idonta Har ta bude duka, Jin An Rike mata hannu Yasa Ta juya idanunta suka Sauka akanshi, Murmushi ya mata sannan Yace "Sannu", Bin dakin tai da kallo, Tunda take ko a kauyen su bata taba ganin daki mai kyau irin Wannan bah, Tunowa datai Ya Tasiu ya taba fada mata Idan Bata daina yawo bah akwai masu Daukan mutum su Ciremai kai shiknan ya mutu, A razane ta mike ta zauna tareda kwalla ihu, Yunkurin Tashi take yayi maza ya riketa Yace "Ina zaki??", Bakiga bakida lapia bah, Ihu ta cigaba har saida nurses Suka shigo, ya kallesu yace "Bkmai you can go" Ganin Nurses Din da Fararen kaya yasa ta kara tsurewa, Janye hannunta tai daga nashi, Tana Kiran ya tasiu dakarfi tareda fashewa da kuka, Yace "Come down am nt here to hurt you" Ganin batamai magana bah Yasa yayi Tunanin Ko batajin Turanci da Hausa, Tunanin Shi ko Bafulata na neh, Ganin yanda takeda haske sosai da yalwataccen Gashi, Dafe goshin shi yayi Yace "Ya Salam" Ya zanyi da yarinyan nan, Jin Muryanta Yayi Tana cewa "Dan Allah karka Ciremin Kaina dan Allah"

Ummu Farheen✌🏻
        N
Aysha Gana💕
[10/15, 7:38 AM] ‪+234 813 184 5457‬: [9/3, 6:00AM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
             N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*51to 55*

Dan Kallanta Yayi Sanan Yace "Kinga Ina Miki Kamada Masu cire Kai neh??" Ga Mamakinshi Kanta Yaga ta Daga Alamar "Eh", Kara kallan jikinshi Yayi Sannan Ya kalleta, Kokarin Saukowa take daga Kan gadon Tana kuka a Hankali, Wannan Karan Beyi Yunkurin Hanata bah, Zafin Dataji a kafafuwanta Yasata cewa Ouch!, Kasa Kasa Ya Kalleta Yace "Ina zaki??" Hawayen Fuskanta ta goge Tace "Ni Dan Allah karku Ciremin Kaina Ban muku komai bah"..

Dan Murmushi yayi Sannan Yace "Kinga Ina miki Kama da Dan Yankan kai neh??" Kai ta gyada Alamar Eh, Karasawa Yayi kusada ita Yace "Nan Asibiti neh, Jiyan on my way home na bigeki da mota Shine na kawoki nan" Ta kuramai Ido Tana Kallanshi, Kyafta mata ido Yayi Sannan Yace "Koh baki yarda bah" Murmushi tai Dan ya Tuno mata da Ya tasiu, Ta turo baki Tace "Tho ina Ya Tasiu??" Yace Ina Yaje??..

Batace Komai bah Sai Yatsine Fuska datake Tana Kallan Kafarta, Ya Lura da hakan Yace "Yana Miki Zafi neh??" Langwabar da kai tai Idonta ya ciko da kwalla, Ya Xauna kusada ita yace "Sorry Zai daina kinji??" Shafa Cikinta Tai Ta Kalleshi tace "Yunwa nakeji Yaya", Dan Murmushi Yayi Yaji dadin Maganan data Fada, Ya fita dasauri...

Tana Ganin Ya fita Ta mike Dakyar Tana dangyashi Hawaye Na zuba a idonta, Ta fita tana Dube dube, Mutane ta gani Burjik Kowanne na harkan Gabanshi, Kofan dataga Anabi Shi itama tabi, Haraban asibitin ta fita, Motocci Burjik Tagani a Haraban Asibitin anyi parking, Hango titi tai Motocci nata wucewa, Kyalkyalewa Da dariya Tai Sannan Tace "Lah Mota Irin Na Alhaji" Muryan Naeem taji kusada ita Yace "Oh! Thank God! Na dauka kin gudu ne" ya tsuguna A gabanta ya rike Kafadanta Yace "Dah Ban ganki bah bansan Halin Dazan shiga bah" Kuramai Ido Tai Batare datace komai bah, Hannunta Ya kama suka koma Dakin Sai Turo baki take, Zaunar da ita Yayi yace "Menene Kike Fushi" Cikin Muryan kuka Tace "Ban gama Kallan motocin bah" Dan Murmushi yayi Yace "Kinaso kiga Motocci?" Kai ta gyada mai Dasauri Yace "Ok tho ki Fara Cin Abinci Kinji" Take Away ya aje Mata, Plantain ne Dakwai sai Chips a gefe, Kallanshi Tai Tareda murmushi tace "Nawa neh?" Kai ya Gyada Yana kallanta, Aiko Ta fara Ci Sosai, Hannu Baka hannu kwarya, Kallanta yake Cikeda Tausayi harta Gama sannan tadauki Tea Tasha tana lumshe ido...

Saida Ta Gama Ya Kalleta Yace "Menene Sunanki?" Tace "Tasneem" Woaw! Nyc Name" Tace "Tho kaifa?" Yace Sunana "Naeem" Gani Kawai Yayi ta kyalkyale da dariya Sannan Tace Sunan Turawa" Murmushi Yayi yace "Ina zaki Jiya naganki A hanya har na bugeki" Sai a Sannan ta tuna Tai narai narai da ido Tace "Koba Iya bace zatamin Aure" Ya xaro ido Yace "Aure!?" kaita gyada, Shiru Yayi baice Komai bah Har na Wasu lokuta..Ta kalleshi tareda Langwabar dakai tace "Zanyi Fitsari" Ya Nuna mata toilet Yace Gashi Chan" Tana shiga ta fito Tace "Tho aina zanyi? "Yanzu ya gane daga kauye take, Dakanshi ya nuna mata komai sannan ya Fito, Fita Yayi daga Dakin Yaje Nursing Station, Wasu Nurses yasamu Yace Dan Allah su Lura da ita Zaije ya dawo, Dasauri suka amsa Ya fita ya nufi Motarshi...

Gida Ya nufa Yayi Wanka, Ya fita ya Nufi Wani Eatry nan Kusa, Saida ya karya sannan yama Tasneem take Away Ya fito, Saida Ya Tsaya a wani bouque Ya sai mata Readymade kaya Da English Wears sannan ya karasa Asbitin...

Ummu Farheen✌🏻
         N
Aysha Gana💕
[10/15, 7:39 AM] ‪+234 813 184 5457‬: [9/3, 1:45PM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
              N
Aysha Gana
+2347017251433

*56 to 60*

Motan Dr Sa'ad Ya gani a Haraban Asibitin, Yadanyi Murmushi Sannan Yayi Parking Ya Shiga, Office dinshi Ya nufa Da Sallama, Patient ya gani Kwance Yana Dubawa, Yace Oh! Sorry doctr Barinje in Dawo, Dr Sa'ad Yace "Ok no Problem" Ya rufe Sannan Ya nufi Dakin da Tasneem take...

Kwance Ya sameta Tanata Barci Hankalinta kwance, Ya karasa ya zauna Akan Kujeran dake Facing gadon, Kura mata Ido Yayi sannan Ya saki Murmushi, A Ranshi Yace "Sleeping Beauty" Hannu Yasa Ya Cire Gashin daya Rufe mata Fuska, Knocking yaji a kofar Dakin, Ya mike dasauri Sannan Yace "Come in"...

Wata Nurse ce Ta shigo Tace "Good Morning Sir!" Yace "Morning"..Tace "Sir Patients are Waiting For You" Osh! Yace Tareda tafe Kai, Ya juya Ya Kalli Tasneem Sannan yace "Ok lets go" A Tare Suka Fita, Office dinshi Ya nufa, Aiko Yaga Patients Dayawa a bakin Kofar kowa burinshi Dr Naeem Ya dubashi, Saboda Shine Sabon Doctr dinda Aka Kawo Asibitin, Bude Office din Yayi ya shiga Nurse na biye dashi Rike da Folders din Patients din..

Haka Yayi ta dubasu Anma hankalinshi na Gurin Tasneem, Yana Cikin Duba Na karshe, Ya kalli agogo Karfe Daya saura, Yadanyi Tsaki yace "Am gonna Miss Zuhur" Patient din Wanda Yake bah musulmi bah Yace "Ok Give mie the prescription" Kan Naeem Yayi Magana aka Turo Kofan Office Din..

Dagowa Yayi Suka Hada ido da Tasneem, "Murmushi Yayi sannan ya karasa Rubutun ya mika mai" Ya tashi Yabar Office din, Tasneem Ko sai bin Office din take da kallo, Yace "Ya akai kika san Ina nan?" Murmushi tai tace "Ni bansan Kana nan bah, Kawai ina Bude Kofofin ne ina dubawa inga meke Ciki" Dan murmushi yayi Yace "Kinci abinci??" Kai Ta girgiza Alamar Aa, Yace "ok" Hannunta Ya kama suka Koma Dakin, Ya zaunar da ita sannan ya bata Abincin, Ta amsa tana Murmushi Sannan ta fara ci..

Kayan daya siyo mata ya nuna mata, Ta amsa Tana dariya Ta kalleshi Tace "Nawa neh?" Kai ya Gyada Ya mike dasauri yace Barinje Masallaci, Ya fita dasauri dan Yakusa Rasa Sallah..

A hanya Suka hadu da Dr Sa'ad, Doctr Yace "Ya Akai dazu naga kana nema nah, Yace "Oh! Baka Rubuta ma Tasneem komai bah Na bangaren Magani", Dr Sa'ad yadan harareshi yace "Tho kai meye aikin kah" Naeem yace "Tho ai kai ka duba tah" Dr Sa'ad Yace "Tho abarta haka" Yabar wajan Yana hararan naeem yana Murmushi"...

Dakin Ya shiga Ya samu tana zaune tana kallan cartoon tana Dariya, Ya karaso ya zauna Kusada ita Yace "Tasneem!" Batace komai bah hankalinta na wajan Kallon datake, Dan tabata yayi ta zabura da Dasauri Yace "Waya kunna Miki tv?" Tace wata ce, Shiru Yayi ya kura mata ido Kayan sun mata kyau Sosai, Yace "Tashi muje Gida, Ta juyo ta kalleshi a tsorace Sannan ta Fashe da kuka tace "Ni baxan koma Wajan iya bah Dukana take Kuma zata min Aure, Baice komai bah sai Kayanta daya siyo ya har hada ya Kalleta Yace "Tashi muje" Maqe kafada tai tana kuka ahankali, Duk ta Bashi tausayi Yace "Muje mana" Ta mike a Sanyaye tana cigaba da kukan, Office din Dr Sa'ad ya leka yace "I Will be ryt back" Dr Sa'ad Yace "Tho"..

Dakanshi ya sata A motan Suka bar Asibitin, Saida Ya tsaya wani Babban Pharmacy ya Sai mata magun guna Sannan suka dau Hanya "Itadai Tasneem kanta na kasa tana kuka Kamar ranta zai Fita" Lokaci Lokaci yakan kalleta Ranshi na soya sam baisan Jin Kukanta, Buh he dnt Hav any Option"

Ummu Farheen✌🏻
         N
Aysha Gana💕
[10/15, 7:42 AM] ‪+234 813 184 5457‬: [9/5, 6:12AM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
             N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*61 to 65*

Gudu Naeem yake Sosai Jefi jefi yake kallan Tasneem wacce har yanzu kuka take bil hakki da gaskiya, Jitai Ya Tsaida Motan Hakan Yasa ta dago dasauri, Ga mamakinta Sai tagansu a bakin Wani makeken gida, Juyawa Tai ta kalleshi Suka hada ido Sannan Yayi Horn Mai gadi ya bude, Shiga yayi yasamu guri yayi parking..

Kallanta Yayi Yace "muje" Bah musu ta bude Murfin motan kamar yanda taga yayi dazu ta Fito, Hannunta Ya rike Tana Dangyashi Har suka Karasa Bakin kofan Falon, Key a ciro A aljihu ya Bude Sannan Ya jata suka shiga, tsayawa Tasneem tai tana Kallan Falon, Tunda take a rayuwar ta bata taba ganin Falo mai kyau irin Wannan bah, Kasa Jurewa tai ta Kalli Naeem wanda Ya nemi guri ya xauna yana kallanta tace "Nan Gidanku neh??" Kai ya gyada yana Murmushi tace "Meh yasa a garin mu babu irin Wannan dakin??" Kafada ya daga Yace "Nima bansani bah" Zoki Zauna Nan Ya nuna mata kusa dashi, Bah musu ta zauna Sannan Tace Ina Yayanka?? Kokai bakada Yaya??

Dan Dariya yayi Yace "Banida Yaya, Saidai in ke zaki zama yayana" Dariya tai Tare da rufe bakinta tace "Lah! Kato dakai kace nice yayanka" Murmushi Yayi har saida Fararen Hakoranshi Suka baiyana, Yace "Tho menene a ciki" Ta kara kallanshi Tace "Tho ina Mamanka da Babanka??" Tambayar tazo mai a bazata Anma saiya Share Yace "Basa nan" Suna Ina ta kara Tambaya, Mikewa Yayi yace "Umm idan na biyema Tambayanki Bazanyi komai ba, And i have to go back to my office"..

Tadanyi Narai Narai da ido Tace "Ya Naeem?" Ya Kalleta Fuskarshi Dauke da murmushi, Yanajin Dadin Yanda take Kiranshi Yace "Na'am Tasneem" Tace "Ya Tasiu Nakeso nagani" Kurrri Ya mata Kana Yace "Tho kinsan inda yake?" Kai ta gyada Alamar Aa! Yace "Tho Kin Gani, Yanzu ki bari idan kin kara Jin sauki saina Maidake Gida Koh, Ihu ta Saki da karfi Sannan ta fashe da Kuka Tace "Wallahi bazan koma bah ni banaso iya dukana takeyi" Zama Yayi Kusada Ita Hankalinshi a tashe Yace "Its Ok"..

Rungumeta Yayi a kirjinshi Yace "Ya Isa Tasneem banason kukan ki, Ta dago tace "Ya Naeem dan Allah karka Kaini Gida Banso" Hannu biyu yasa Ya Tallafo Fuskarta Yace "Tho Tasneem idan ban kaiki Gida bah ta Yaya Zan san Inda Ya Tasiu Yake??" Batace Komai bah saima kuka data kara Fashewa dashi...

Hannu yasa Ya goge Mata Hawayen Yace "Ya isa Tho kiyi Shiru, Hannunta Ya rike Suka nufi Wani daki, Ya bude Suka shiga, Gado ne Babba sai Mirrow da warddrop, Komai na dakin Pink, Tasneem batasan Sanda ta saki Wani Lallausan Murmushi bah, Naeem ya juyo Ya Kalleta Yace "Nan neh dakinki kinji, Kai ta gyada Tace "Nagode" baice Komai bah Ya Karasa da Ita Toilet din Yace "Ai na koya miki yanda ake anfani dashi koh? Kai ta gyada Alamar eh, Yace "Tho Ki kwanta kiyi Barcin ki ni zan koma Asibiti"...

Dasauri ta mike Tana Mutsutsuka Ido da Hannu, Naeem Yace "Menene?" Cikin Muryan kuka Tace "Nidai bazan zauna ni kadaiba Tsoro nakeji" Shiru Yayi Tareda Kura Mata Ido, Yace "Tho Muje" Hannunshi ta kama Suka Fito Ya rufe Gidan Suka Koma Asibiti...

Kwanan Tasneem Uku a Gidan Naeem, Kullum Idan Zashi Office Tare Suke Zuwa, Tana Gefenshi a zauna idan kuma ward Round zashi Kafarta kafarshi, A Cikin Kwana Uku Sun Shaku Sosai, Har Naeem Ya Saba Da Tambayan Tasneem da Surutun ta...

Yauma Kamar Kullum da Sassafe Ya tashi Ya Shirya Cikin black Suit da purple Shirt Sai Red Bode Tie, Kayan sun Amshe Shi Sosai,  Dakin Tasneem Ya nufa, Knocking yayi Ya Shiga, Tsaye ya Sameta Gaban mirrow Ta rike Kugu Sai Jujuyawa Take, Dariya yayi kasa kasa Sannan Yace "Kin shirya shine Baki fito bah" Yau inada Theater ne Kiyi sauri" Sai a Sannan ta juyo Tana Murmushi tace "Ina Kwana Ya naeem" Lapia lau Yace ya kama hannunta suka Fito, Mota suka Shiga Suka nufi Asibiti, Office dinshi ya kaita Ya Dau waya yayi mata Oder din Abinci Sannan yace "Za'a kawo miki abinci Yanzu, Ki zauna A nan kar kije ko ina, Kai ta Gyada yace "Nan da awa biyu ko daya zan dawo kinji?" Tace Tho ya fita dasauri yana mata Murmushi...

Theater Naeem Suka shiga na wani Mutun Mai Fama Da "Bone Tuberclosis" Wanda Ya kama mai Spinal Cord dinshi, Likitoci ne burjik a Theater Room din Saboda bah Karamin Aiki bneh, Sunkai Gurin Awa Hudu da Wani abu sannan Suka fito, Hankalin Naeem Na Wajan Tasneen dan Yasan Yanzu Ta Gaji da jiranshi Myb ma tai Barci, Office dinshi Ya shiga Kai tsaye Anma bah Tasneem, Gabanshi ne Ya Fadi dam! Ya fita Dasauri, Dakunan Patients zuwa Office din Likitoci Naeem keta Shiga Hankalinshi a Tashe Anma bah Tasneem Bah Alamar ta, Dagudu ya fito haraban Asibitin Yana dube dube, Sam Bata a Wajan, Baisan Sanda ya daura hannu akai bah Cikeda damuwa Yace "Tasneem Dnt Lyv Mie, I Rilly Love You and Care about you, I dnt want to loose You, Pls tasnee Come back to mie"

Ummu Farheen✌🏻
           N
Aysha Gana💕
[10/15, 7:44 AM] ‪+234 813 184 5457‬: [9/5, 8:12PM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
             N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*66 to 70*

Idonshi ne Ya Ciko da Kwalla, Ji Yayi an Dafashi Ya Juya A hankali Yace "Tasneem Meyasa Zakimin Haka Har kinsa Hankalina Ya tashi" Ga mamakinshi Dr Sa'ad ya gani Tsaye, Yadanyi Tsaki a hankali Sannan Ya kauda Kai, Dr Sa'ad Yadan Yi Murmushi Yace "Dr Naeem! Uh are in Love, Woaw! Buh kasan Menene?", Tsaki Naeem Yaja Cikeda Damuwa yace "Pls kabarni naji da abinda ke damuna" Dr Sa'ad Yace "Meke damunka?" Naeem ya kalli Sa'ad Yace "Banga Tasneem Bah"...

Murmushi Dr Sa'ad Yayi Ya Riko Hannun Naeem Zuwa Parking Space din Asibitin, Gefen Wata Mota Naeem Ya ganta Tana Xaune a kasa Taba Rubutu akan Wani Farin Paper, Dagudu Naeem Ya karasa kusada Ita Ya Tsuguna Tareda rungumeta, A Hankali Ya Furta "I love You Tasneem, I dnt want to Loose You"  Ta dago ta kalleshi Sam bata gane me yake nufi bah, Turo Baki Tai idonta Ya Ciko da Kwalla Tace "Shine ka tafi ka barni koh?" Yayi murmushi Ya Lakacin Hancinta Yace "Am Sorry Yi Hakuri kinji my Luv" Batace komai bah ta cigaba da Abinda take a papern..

Yace "Kin Tayar min da hankali my Love inata nemanki, Meyasa kika fito?" Ta Turo baki sannan tace "Bakomai" Yace "Tho karki kara kinji?" Har Kinsa Hankalina Ya tashi, Banaso ki kara, Ina Sanki Banaso na Rasaki, Juyowa Tai ta Kalleshi Tana Murmushi Tace "Nima Ina Sanka tunda kana Siyo min Nono mai Sanyi"..

Zaro ido yayi Cikeda Mamaki Yace "Dagaske kina Sona?" Kai Ta gyada, Murmushi Yayi Yace "Tho Taso Muje" Ta mike Ya rike Mata Hannu, Dr Sa'ad Ya gani Tsaye Yanata Kallansu Yana Murmushi, Naeem baice Komai bah Suka Koma office, Duba patients ya cigaba Tasneem na Gefenshi Tanata rubutu A Jikin Papern nan...

Abinci ya musu oder aka Kawo Sukaci Sannan Suka Kama Hanyan gida, Suna hanya Ta kalleshi Tace "Ya Naeem"  idonshi nakan Titi Yace "Na'am My Love" Tadanyi Shiru Sannan tace "Zansha Nono Mai Sanyi, Dariya yayi Sosai Yace "Ice Cream Sunanshi" Ta turo baki Tace "Shi din Dai" Tho Yace, A Wani Hadadden Eatry Ya tsaya ya kalleta Yace "Ina zuwa" Tho Tace Ya fita Ya Shiga cikin Wajan...

Tana Zaune a motan Taga Wani Mota Tai parking Kusada nasu, Juyawa tai Ta kalli Motan aiko Sukai Ido Hudu da wanda ke Cikin Motan, Saurayi me Wanda bazai wuce Sa'an Naeem bah, Fari ne Sosai dogo, Yanada Yalwatacen Gashi a kanshi Kamar Na Yan india, Kurrri Ya mata Yana Kallanta, Kauda kai tai Tana Kallan Takardan Dake Hannunta, Ya Fito daga cikin Motan Tareda Danna Security, Wayanshi ne Ya soma Ringing Ya Sa hannu a Aljihu yana Kiciniyan Cirowa, Dai dai nan Naeem ya shigo motan Yaja Suka kar Wajan, Suyawa tai A Hankali Suka ko hada ido dashi hannunshi a Kunnenshi Alamun Yana amsa waya...

Naeem yace "Meh kike Kallo?" Ta turo baki Tace "Wani ne Kaman Bature sai Kallona Yakeyi" Murmushi Naeem Yayi yace Kodai Ke kika Kalleshi?? Girgiza Kai Tai Tace "Aa!" Tho kawai Yace Ya Kara Jan Motan Sukai gida..

*Shin Wanene "Dr Naeem"*

Alhaji Umar Zaza Shine Asalin sunan mahaifinshi, Haifafen Karaye ne Dake jahar Kano, Mahaifiyar Naeem Yar Asalin Kasar Mali Ce, Alhaji Umar Shi kadai ne Yajan iyayenshi, Yanada Shekara Ashirin da Uku Iyayenshi duka Suka Rasu, Cikin ikon Allah Ya Tafi Mali Karatu inda Anan suka Hadu da Hajiya Zainab, Allah Ya hada jininsu Har yakaiga aure, Sun Dade Allah bai basu Haihuwa bah har sun Cire Rai Allah ya Albarkace su Da Naeem, Tun tasowan Shi Yake Cikin Gata da Soyaiyar Iyayenshi, Ya samu ilimin Addini Sosai, Yanada shekara Goma Sha biyu Yayi Sauka a lokacin Alhaji Umar ya samu Aiki A China "Beijin" Inda dukansu suka koma Chan, A nan Naeem Yayi Makarantan shi Na likita a "Liaoning University of Technology" dake China, Tun yana Karatu yake burin Yin Aikinshi a kasarshi nigeria Saboda Taimaka ma Talakawa Marasa Karfi, Zuwanshi Nigeria da Sati Daya Allah Ya hadashi da Tasneem Yana dawowa daga Asibiti..Wannan Knan..!

*A Gangara fah?*

Da Sassafe iya Ta tashi Ta fita nemo dan Hatsin da za'a Girka Saboda makota, Salame ko kwana tai kuka tana Tunanin Tasneem dinta, Tasan Ruwa ya gama Mata Duka, Shatu ce ta Fito Ta leka Dakin Su Tasneem Bataga kowa bah, Ta dawo tsakar gidan Ta soma Kwala mata kira, Anma Shiru, Salame ta leko Daga dakinsu Tace "Kila Tabi iya ne Ki jira mana ta dawo" Shatu ta Galla ma salame Harara...

Tara da Wani Abu na Safe Iya ta shigo gidan Tana washe baki, Shatu tace "Ina Amaryan?" Iya tace "Bangane ina amarya bah, Ina taje?" Shatu Cikeda mamaki Tace "Tun Safe fah bata Gidan nan na dauka tare kuka fita" Iya ta girgiza Kai sannan tace "Bah tare Muka Fita bah" Kin Duba Dakinsu?? Shatu Tace "Ai Sai kuma kiyi"..

Tashi Iya Tai duk inda Tasan Tasneem na zama a cikin gidan sun duba bata nan, Hankalinsu a tashe Musamman ma Salame Suka hau duba gidajen Makota Anma bah Tasneem, Salame na kuka Tana Shiga gidan kawayensu na islamiya, Duk Wacce Ta tambaya sai tace "Tah dade bata ganta bah", A haka Har Suka gaji suka dawo gida Cikeda tashin hankali..

Ummu Farheen✌🏻
         N
Aysha Gana💕
[10/15, 7:46 AM] ‪+234 813 184 5457‬: [9/7, 7:35AM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
             N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*71 to 75*

Shatu ce Tai Karfin Halin Cewa Yanzu iya a haka za'a Daura Ba'a Ganta Bah, Iya Ta Girgiza Kai tace "Ina fah ai kuma bah daura aure" Itadai Salame ba abinda take Sai Kuka...

Makota ne Suka Fara Shigowa Sanya Alheri, Nan Mummunan Labari Ya Riske Su, Nan Fah Aka Koma Jaje, Kankace Meh Labari ya bazu na bacewan Tasneem, Alhaji Najin Haka Ya taso dakanshi Yasamu Iya, Labarin Karya da gaskiya ta fadamai, Yako Hada Rai Yace "Abashi kayanshi" Iya bataso bah Hakanan Ta Tattara kayanshi ta bashi, Har Kudin Daya bata Saida Yace Tabashi abinshi, Dole Ta shiga makota tayi rance Ta kawo mai ya buga Vespan shi Yabar kofar gidan...

Kwanan Mallan Uku Ya Dawo, Tun A hanya Aka Shiga mishi Jaje, Abin Ya Matukar daure mai kai Hakanan Ya karasa Gida, A Tsakar gida Ya Soma Kwallawa Iya Kira, Ta fito Jiki na Rawa dan Tasan Kiran nan bah lapia, Ya Kalleta Jikinshi na Rawa Yace "Ina Tasneem?" Shiru Tai Kanta a kasa, Dakarfi yace "Magana fah nake miki koh bakiji" Ta Fashe Da Kukan Karya tace "Tasneem Dan Kawai na Mata fada akan Fita Yawon dare da take Shine Tasa kafa ta Fita" Girgiza Kai Mallan Yayi Yace "Kin Cuceni! Kinci amana, Yanzu da wani ido zan kalli yayan Yarinyan nan Wanda ya damka min Ita Amana"...

Hawaye ne Ya soma Zarya A fuskan Mallan, ya Kalli Iya Yace "Zama na dake ya kare a cikin Gidan nan, Kije na Sakeki Saki Daya" Ihu Ta Fashe dashi Ta Karaso tana kokarin Riko mai Kafa Yabar Wajan dasauri, Har xai Shiga Dakinshi ya Juya Ya kalleta Yace "Karki Barmin Yaro ko daya ki tattara su kubar min gida yanzun nan" Ta kara Fashewa Da kuka tana bashi Hakuri, Shatu da Salame suka Fito Suna Kuka, Salame ce Ta shiga dakin Mallan da Sallama...

Ya Amsa bah Tareda Ya Waigo bah, Kuka Take Tana Bashi Hakuri, Bai Kalleta bah Ya Juya fuska hawaye na Gangarowa daga idonshi, Yace "Salame Har dake za'a Hadu a kori Tasneem daga idan nan?" Kuka Ta kara Fashewa dashi taba Mallan Labarin komai, Mallan Ya Rintse ido Hawaye Suka gangaro mai Yace "Talatu Kin Cuceni"..

Hannun Salame Yaja Suka Fita Ya Rufe Dakin Ya barta nan Sannan Ya Kalli Iya Yace "Kar in dawo in sameku a gidan nan" Ya fita Fuuu, Bai Dawo Gidan bah Sai Shadaya da Wani abu na Dare, Bai Gansu bah kuma Dakin a bude, Daga Labulen Yayi yaga sun kwashe Komai, Yayi Tsaki ya Shiga dakinshi Ya Kwanta, Washe Gari da Sassafe ya nufi gidan Kiya taka Yace Ya Saki Gida, Sannan ya koma Ya kwashe Kayanshi Yabar gidan..Tho Pha!

          *****

Yau Sunday Naeem baida zuwa Asibiti dan Haka Barci yakeso Yayi Sosai, Yana Kwance wuraren Karfe Bakwai na Safe ya jiyo karan Tv, Ya Fito dan Yasan Ya kashe Sannan at dis tym Tasneem bata Tashi bah, Jallabiya ya zura ya fito, Tv Ya hango kunne da Mbc 3 channel, Ya karasa Cikin Falon aiko yaga Tasneem Zaune Ta kurama Tv Ido, Ya Karasa Ya kashe Tv Yace "Har kin Gama barcin neh??" Gyada kai tai Tana turo baki, Yace "Aa ki koma ki kara koh yunwa kikeji?" Girgiza kai tai Alamar Aa! Sannan Tace "Ni Ya Naeem Kallo Zanyi" Yace "Haba My Love ki karayin Barci Anjima Sai muje na miki Shopping din koh" Bah Kince Harda Yar Tsana Kikeso bah? Kai Ta gyada tareda Murmushi Yace "Muje"..

Bah Musu Ta Tashi Tare da Rike Hanunshi Ya Kaita dakinta, Saida Yaga ta kwanta Sannan Ya Fito ya Koma dakinshi, Jallabiyan Ya cire Ya Fada Gado Yace Wash! Ko Minti biyu beyi bah ya Karajin Muryan Tv, Zaro ido Yayi Yadau Jallabiya yasa Ya fita, Zaune Yasameta Tana kallo tana Dariya, Ya karasa Ya kashe Tv Yace "Barcin kenan" Turo baki tai ta mike ta koma Dakinta, Shima Dakin nashi ya koma...

Jallabiyan Ya cire bai kaiga Hawa Gadon bah ya kuma Jin Karan Tv Na yanzu ma kure Volume akai, "Oooh My love" ya fada Da Karfi, Ko Jalabiyan baisa bah Daga shi Sai Boxers Da Singlet, Tana ganinshi Tai Hanyan Dakinta dagudu, kamota Yayi Yace "My Love bakya ji koh?" "Bakyaso nai barci?" Ta Turo baki Tace "To Ya naeem ni banajin Barci" Murmushi yayi ya Kwaikwayi Muryanta da yanda Tai yace "Tho Ya Tasneem ni inaso nai barci" Dariya ta Fashe dashi Dimple dinta Suka Lotsa, Kurri Ya mata Yana Kallanta, Santa Da tausayinta ke Kara shigarshi..

Duk Sanda Yake Tareda Ita Yakanji Farin Ciki, Yace "Tho Yi hakuri ki koma ki kwanta kinji my Love" Maqe Kafada tai Alamar Aa! Yace "Waima Waya koya miki kunna Tv?" Tayi Murmushi Tace "Naga Yanda Kakeyi neh", Yayi Murmushi Yace "Duk Sanda kika kara Kunna Tv din nan, Ya dan Ja Hancinta Yace "Wannan Dogon Hancin Zan Cire" Murmushi Taimai, Shima Murmushin Yayi Yace "You Look Cute Wen uh Smile"...

Tuna Batasan meyace bah Yasa Yace "Kina Zuwa School a Kauyenku?" Kai ta gyada yace "Wanne Class kike?" Yace primary five" Jinjina Kai Yayi Ya mikar da Ita yace "Muje ki kwanta pls" Ta mike Ya Rakata Ta Koma Sannan Ya koma Nashi, Kwaciya Yayi Barci Koh Ya daukeshi..

Chan Cikin Barci Yaji wani Abu A Kunnenshi Kamar Kwaro yana komarin Shiga, Ya mike a Tsorace Yana Taba Kunnen, Fashewa Da dariya Tasneem Tai Tace "Kaima Babba Kanajin Tsoro" Murmushi kawai ya mata, Haka ta Dingi Damunshi Barcin Dabaiyi ba Knan, Dakanshi Ya hada Musu Breakfast Sukai Sannan Yace Taje Tai Wanka su Tafi, Tsalle Tai Cikeda Murna ta Mike Ta nufi dakinta, Wayanshi ne Yadau Ringing Ya Duba Sannan Ya dauka Ya kara A Kunne...

Ummu Farheen✌🏻
         N
Aysha Gana💕
[10/15, 7:49 AM] ‪+234 813 184 5457‬: [9/7, 6:23PM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
             N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*76 to 80*

A Hankali Yace "Mum Good Morning" Daga Chan Bangaren Tace "Son Kadai Manta Dani Kwana Biyu, Kullum Dasafe Saika Kirani Before you go to work anma Ynxu ka Daina" Naeem Yace "Oh No Mum Its not What Uh Think, Aiki ne Yamin Yawa Dats Why buh am Sorry and..." Tace " And What Son?? Tel Mie" Shiru Yayi Sannan Yace "Mum I Mistakenly Hit a gurl Wen am Going Back Home Last Week" Innalillahi Wa Inna Ilaihi Rajiun Tace Sannan Takara Cewa "Ina Fata ba wata Matsala Bace Babba, And pls dnt Tel mie Ta mutu" Dan Murmushi Yayi Jin yanda Ta rude Yace "No Mum Har Tama Warke, She's here Wit Mie"..

Cikeda Rashin Fahimta Tace "What Did uh mean She's Wit You?" Yace "Mum Daga Kauye Take Batada Parents Sai Guidiance and Suna Gana Mata Azaba Its Why, She's Very Young just 11yrs", Hada Rai Tai Kamar Yana Kusada ita tace "Ban Yarda bah kuma ban amince bah, Dole ka maida ita gurin Koma Waye Nata, Haba Son What did You Think ppl wl say" Yayi Shiru Baice Komai bah, Tace "Dan Haka Gobe Nakeso ka maida Yarinyan nan, Kuma Sai Dad dinka Yaji, Sanin Kanka neh Banason Talaka" Wai Meyasa Naeem bakajin Magana neh?" Baice Komai Bah Ta gama Ta Kashe Wayan..

Shiru Yayi Ya Dafe Kanshi, Inna Lillahi Wa inna Ilaihi Rajiun!, Why Mum! Why!!, Meyasa kikeson Rabani da Tasneem, I Love Her I Dnt Want To Loose Her, Dora kanshi Yayi Akan Dinning Din Yayi Shiru, Dagudu Tasneem ta Fito Sanye da Afterdress Baki Sai ta daura Gyalen Kayan a Kai, Ta Karaso Kusada Shi ta Dafashi Tace "Ya Naeem Nagama muje" Dagowa Yayi Ya kalleta Idanunshi Sunyi Ja, Ta Kalleshi Tace "Ya Naeem Bakada lapia Neh??" Baice mata Komai Bah sai Hawaye ya gangaro Daga Idonshi, Zaro ido tai, Itama ta fashe da Kuka tace "Menene Ya Naeem??" Kaima Zaka Tafi ne Kabarni Kamar yanda Ya Tasiu Ya tafi??"..

Baice Komai bah ya mike Ya Shiga Dakinshi, Zama Tai a wurin Ta saki kuka, A nan Taci kukanta Har Barci ya dauketa, Abin Duniya yayima Naeem Yawa, Wayanshi Ya Dauko Ya Danna Layin Sa'ad, Bugu Daya ya Dauka, Cikin Wani Irin Murya Naeem Yace "Dr Kana Gida neh??" Sa'ad Yace "Lapia dr Naeem" Naeem Yace "just Answer mie" Eh Dr sa'ad Yace Naeem baice komai bah ya kashe kiran..

Yakai Kusan Minti Biyar A kwance Dakyar yasamu Ya Tashi Ya Shiga Toilet, Wanka Yayi ya fito, Blue Jeans Yasa Da Black Top, Feshe Jikinshi Kawai Yayi da Turare Ko Combing Kanshi beyi Bah Ya fito, Kwance Ya sameta gefen Dinning Tana Sharan Barci, Tausayinta Ya kamashi, A Hankalin Yabar Falon Ya Fita, Motanshi Yahau Mai Gadi ya bude mai gate, Yadanyi Slow Ya kalli me Gadin Yace "Pls Ka kula da Tasneem Na barta tana Barci karka bari taje koh ina" Tho An gama ranka ya dade Cewar Mai gadin, Ya fita Yaja Motan Dagudu..

Gudu Yake Sosai Har Yakai Gidan Dr Sa'ad, Horn Yayi Mai gadin Ya bude Mai Gate ya Shiga, Parking Yayi sannan Ya Kira Dr Sa'ad A waya Yace ya Shigo, Dasallama Ya Shiga Falon, Zaune Ya Sameshi Shida Matarshi da dan karamin Dansu da bai wuce Shekara uku bah, Suka Gaisa Sannan Matarshi ta basu guri, Naeem yayi Shiru Yana Wasa da car Key dinshi..

Sallaman Matar sa'ad Yasa Yadan dago tareda Amsa wah, Tray ta aje Cikeda Kayan Ciye Ciye, Ya kalleta Yayi Murmushi Yace "Dama kin Barshi am Ok" Tace "Lallai ai ba'a zuwa Nan gidan ba'aci abinci bah" Baice komai bah Ta Tashi Tabar Wajan, Sa'ad Ya kalli Naeem yace "Whts Wrong Naeem, Naganka Cikin Damuwa, ina Tasneem?" Tana Gida Kawai Yace, Sa'ad Ya matso Yace "Naeem Fadamin meke faruwa?" Ya dago ya kalli Sa'ad idonshi ya ciko da kwalla yace "Zasu Rabani Da Farincikina Sa'ad, Ya rikemai Hannu yace "Pls Sa'ad Karka bari Su rabani da ita I So much Love her pls"...

Sa'ad Yace "What Did You Mean Naeem Yimin Bayani Yanda zan ganeh, Labarin Tasneem kaf Yaba Sa'ad Sannan ya Fadamai Yanda Sukai da Mum dazu, Ajiyan Zuciya Sa'ad Yayi yace "Naeem dole kabi Umarnin mahaifiyan Kah, Menene Abin Danuwa ai Babu komai Idan ka maida ita Saika Rinka zuwa dubata koh" Girgiza Kai Naeem Yayi Yace "Sa'ad kaima ka goyi Bayan na maida Tasneem Haba mana Sa'ad, Ina Santa, Ina Tausayama Rayuwarta, Inaso Nasama Mata farinciki, Inaso Na Zame mata Kamar Iyayenta Data rasa, Shiru Sa'ad Yayi Cikeda tausayin Abokin Nashi, Lallashin Shi Ya Shiga yi akan Ya maida ita inyaso Ya rinka zuwa Yana dubata, Sun Aje Akan Gobe da Sassafe zasu Tunda bah wani nisa baneh...

Tasneem koh Naeem Ya fita ba dadewa Ta Tashi, Dube dube Ta Shiga yi cikin Gidan Dakinshi Ta shiga Bai nan ta Fito ta leka kicin Nan Ma baya nan, Da kuka Ta Fito Haraban Gidan Tana kwalla mai Kira, Ganin bah motarshi Yasa ta Zauna Dabar Ta Saki kuka mai Karfi, Mai gadi ne Ya nufeta Dasauri Yana tambayanta meya Faru? Batace mai komai bah Sai kuka datake tana kiran Naeem, Yace "Yi Shiru Ya fita Neh Yace Bazai dadeba Zai dawo", Dakyar Ya shawo Kanta Ta Tashi Ya kaita Kan benchn Shi Suka Zauna, Ganin Taki Sakin Jiki Yasa Ya Shiga bata taysuniya Tanata Dariya, A Haka Har Ta sake tanata bashi Labarin Kauyensu...

Ummu Farheen✌🏻
      N
Aysha Gana💕
[10/15, 7:50 AM] ‪+234 813 184 5457‬: [9/8, 9:29AM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
             N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*81 to 85*

Sun Dade Yana Bata Tasuniya, Chan Sukaji Horn Din Motar Naeem, Dasauri Mai Gadi Ya bude mai Ya shigo, Turo Baki ta kauda Kai, Parking Yayi Ya fito, Mai gadi yamai Sannu da zuwa, Ya amsa Cikin Sanyin Murya, A Hankali Yace "Tasneem!" Kauda Kai Tai Rungume Hannunta ta Turo baki Tareda Kauda Kai, Dan Murmushi Yayi Ya Karasa Kusada Ita Ya duka Yace "Nayi Laifi My love Bazan Sake bah", Bata Kalleshi bah ta kauda kai, Hannunta Ya rike Ta kwace Ta tashi Ta Shiga Falo, Binta Yayi Ya Sameta Kan Kujera Tanata Kumbure Kumbure, Yayi Dariya kasa kasa Yace "Am Sorry baeby, Kinji!, Kira na Akai a Asibiti kinji", Kai Kawai Ta gyada Tace "Ya Naeem Meyasa kake kuka dazu?, Kaima zaka tafi kabarni ne Kaman Yanda ya Tasiu Ya Tafi?" Gabanshi ne Ya fadi Tuna Kalaman Mum, Ya kirkiro Murmushi Yace "Aa Bazan Barki Bah, I Will Always Be Wit You"...

Murmushi Tai Ta rungumeshi Tace "Ya Naeem Karka Tafi Ka Barni Kaji?" Dakyar ya iya gyada Kai Hawaye Cike a idonshi, Sassauta Rikon Yayi Ya Kalleta Yace "Muje Na Siyo Miki Yar Tsanan Koh?" Dariya Tai Tace "Eh Muje" Hannunta ya Kama har Bakin Mota, Ta Kalleshi Ta Turo Baki Tace "Ni Ya Naeem Wanchan motan zamu Shiga" Ta nuna Heneci arsh, Yace "Tho ai Wanda Zamu Shiga Yafi Kyau da Tsada" Tace "Nidai Wanchan" Yace "Tho An gama My love" Keyn Motan Ya dauko Suka Shiga Yaja Suka bar Gidan...

Suna Cikin Tafiya Ta Kalli Naeem tace "Ya Naeem Nima Ka Koyamin Na Rinka tuka kah" Dariya Yayi A hankali Yace "Tho Zan koya miki anma Bah Yanzu bah" To Sai Yaushe? Yadan Kalleta yace "Sai Kin Kara Girma Kinji?" Kai Ta Gyada Ta maida dubanta ga Titi, Sun Kusa Zuwa Shopping mole Din Ta Kara Haduwa Da Wannan Saurayin, Yana Cikin Motarshi Yana ja anma idonshi nakan Tasneem, Murguda mai Baki tai Ta kauda Kai Tareda Dan Sakin Tsaki, Naeem Yace "Menene kike Tsaki?" Tace "Wannan baturen Na Ranan da Yaketa Kallona Shi na Kara Gani" Yace "Ina Yake?" Juyawa Tai da niyan nuna mai Shi amma Taga Wayam, Juyawa Tayi ko yana Bayansu Anma bata ganshi bah, Tace "Ban Ganshi bah ya Tafi", Kai Naeem Ya gyada Dai dai da Isan Su Wajan yayi Parking Suka fito...

Shopping Sosai Naeem Ya Mata Tun Daga Kan Kayan Sawa Zuwa Kayan Ciye Ciye, Manyan Teddys Ya sai mata guda biyu tanata murna Tanajin Dadi har suka dawo gida...

Dakinta ya kaimata Kayan Ya koma Nashi Dakin, Yana Kwanciya komai ya dawo mai sabo kan maganarshi Da Mum, Dafe Kai Yayi Yace "Mum Why!" Bazai iya Fita ya musu take away bah dan Haka Ya mike Ya hada mata Oat dan Yaga Tanaso Sosai, Ya kaimata, Ta Amsa Tana Murmushi, Saida Yaga Tasha Sannan Ya koma Dakinshi..

Haka Ya wuni Sukuku Har Dare, Saida Ya tabbatar tayi barci Sannan yadau Babban Trolley Ya Shiga Dakinta, Kayanta Ya saka Ciki duka da Kayan Ciye Ciyen Daya Siyo mata, Set Daya ya barmata Wanda zatasa Dasafe, Ya Fita da Trolleyn Yasa a Bayan Booth...Dare ya Tsala sosai Komai Shiru, Duk wani abu mai Rai ya kwanta Yana Hutawa Ko yana barci, Naeem ko Sai safa da marwa yake a Cikin dakinshi, Lokaci lokaci yakan Shafa Gashin Kanshi ya Saki ajiyar Zuciya dakarfi, Dakyar yasamu barci Ya daukeshi..

Da Asusubah Ya Tashi yayi Sallah Yayi Wanka, Dakin Tasneem Ya leka Ya sameta Sai barcinta take, A Hankali ya soma tashinta, Ta Mike Zaune a tsorace Ta kalleshi tana Yatsine Fuska, Yace "Tashi kiyi Sallah Kiyi Wanka Yau Zamuje anguwa da Sassafe" Jin Maganar Yawo yasa ta mike Ta fada Toilet Shi kuma Yabar dakin, Tea Ya hada Mata Da Bread Ya aje kan Dinning, Chan Sai Gata daure da Towel Ya kalleta Yace "Ke Nakefa Jira" Kamar xatai kuka tace "Banga kayana bah" Yace "Wanda xakisa yana kan Gado sauran nakai dakina na boye miki" Tho Tace tareda komawa dakin..

Dafe Kanshi yayi dake Sara mai, Sunan Allah kawai yake Kira a ranshi, Chan Sai gata ta fito Ta Zauna kan Dinning Din, Yace "Ga Tea Bamuda Time" Bah musu Ta dauka ta Fara sha, Chan Ta kalleshi tace "Ya Naeem kai bazaka Sha bah??" Yace "Nasha kafin ki fito" Ta gyada kai Ta Cigaba dasha, Saida Tagama Tas Sannan Ta dau Cup din takai Kitchen Sannan Ta dawo ta dafashi Tace "Nagama"...

Car key Dinshi ya dauka suka Fito, Tana kokarin shiga gaba Yace "Koma baya zan dauki wani Abokina" Bah Musu ta Koma baya, Yaja Motan suka bar Gidan, Gudu Yake sosai akan Titi, Tun Kafin Yakai Gidan Ya kirashi a waya akan ya fito, Suna kaiwa Suka Daukeshi Suka dau Hanya...

Ummu Farheen✌🏻
           N
Aysha Gana💕
[10/15, 7:51 AM] ‪+234 813 184 5457‬: [9/10, 1:37PM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
             N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*86 to 90*

Sa'ad Yadan Kalli Naeem Ya kafta mai Ido Sannan Ya Juya Ya kalli Tasneem Yace "Tasneem Menene Sunan Kauyenku??" Tai Shiru Tareda Rike Haba Tace "Umm Hayin Mallan, Gangara" Sa'ad Yace "Lallai Kice Keh Yar Garin Mallan neh" Murmushi kawai Tai Batace Komai bah, Sa'ad Ya juya ya kalli Naeem Ganin Yanda Hankalinshi Yatashi Yasa Yace "Park the Car let me drive" Bah Musu Naeem Yayi Parking Sa'ad ya amsa Suka Cigaba da Tafiya...

Tasneem Sai kallan Titi Take Tana Zazzare ido, Ganin Sun nufi hanyar Kauyensu Yasa Ta Kwala Ihu Ta kalli Naeem Tace "Ya Naeem Zai Kaini Gida Dan Allah Kace karya kaini" Naeem baice Komai Bah Sai idonshi daya Ciko da kwalla, Maida Kanshi Yayi Yana Kallan Titi, Kuka Tasneem Take Sosai Tana Rokon Sa'ad Akan Ya Tsaya Karya Kaita, Sun Shiga Kauyen Suka Samu Wasu Mutane Zaune, Sun Gaisa Sannan Naeem Yace "Dan Allah Gidan Mallan Ado Ladan Muke Nema" Mutumin Ya musu Kwatance Sukai Mai Godiya, Tasneem Ta Matso Kusada Kujeran Naeem Idonta Taf da Hawaye Tace "Ya Naeem Kaima Zaka tafine Ka barni?" Ya Naeem Su Iya dukana zasu rinka yi, Ta kara fashewa Da Kuka, Rintsa Ido Naeem Yayi Hawaye Suka Gangaro daga Idonshi, A Hankali ya Share...

Wani Razananen Ihu Tasneem Ta Saki Lokacin da Sukazo Bakin Kofar gidan, Sa'ad ne Yayi Parking Ya Fito, Kofar Gidan Sa'ad Ya Shiga doka Sallama, Yakai Kusan Minti Uku Yana Sallama, Wani Makocin Sun ne ya fito Yama Sa'ad Sallama, Sa'ad Ya mika mai Hannu Sukai Musabaha, Mutumin Yace Bawan Allah Lapia?? Sa'ad Yace "Dan Allah mai Gidan nan muke nema" Mutumin Yace "Oh Mallan?" Ai Kwana Hudu Knan da Sakin Gidan, Sun Bar Gidan Gaba daya, Sa'ad Yace "Dan Allah ko ina Ya koma?"...

Mutumin Yace "Gaskiya ban Sani bah, Kamar sabani Suka Samu da Mai dakin nashi, Yace "Bawan Allah kar kace na Dameka, Dan Allah Ko kasan inda Matan tashi ta koma?" Girgiza kai yayi yace "Bansani bah gaskiya, Anma Muje na Rakaku Gidan Mai Gari Killa Yasan Inda suka koma", Sa'ad Yayi Godiya, Dakanshi Ya budemai Kofar Baya Ya shiga, Kallan Tasneem Yayi Yace "Ikon Allah Tasneem Dama Kina Nan??" Bah Inda ba'a Nemeki bah, Itadai Batace Komai bah Sai Share Hawaye Datake..

Mutum Natama Sa'ad Kwatance Har suka iso Fadan, Shiya Fara Fita dan Yo musu Iso, Sa'ad Ya Kalli Naeem Daya Jinginar da kanshi Jikin Kujeran Kamar mai barci Yace "Be Strong pls, Muje Muga Mai garin Coz ance Basa Gidan Yanzu, Naeem Yadan Bude Ido Ya Kali Sa'ad Yace "Muje", Juyawa Sa'ad Yayi ya Kalli Tasneem Yace "Kema Fito" Bah musu Ta fito, Mutumin Ya musu Iso Har Cikin Fadan..

Bayan An Gaisa Aka Gabatar dasu da Bukatansu, Mai Gari Yayi Gyaran Murya yace "Tabbas Mallan Yazo yamin Sallama Akan Zai ba gari, Yace Zai Shiga Chan Burni Anma Lokaci zuwa Lokaci Zai Rinka zagayo Wa", Shiru Sa'ad Yayi Sannan Ya Kalli Naeem, Dakyar Naeem Ya basu Labarin Yanda Akai ya hadu da ita, Mutanen Fada Sai Mai godiya Suke, Daga Karshe Mai Gari Ya yanke Shawaran Zata Zauna gidanshi Har Mallan Ya dawo" Naeem Ya dago Raunanen Idanunshi Ya kalli Mai Gari Yace "Ranka Ya dade Inaso a bani ita mu koma nasata a makaranta, Nayi Alkawari Lokaci zuwa Lokaci Zan Rinka zuwa Inajin Labari ko Yayanta Ya Dawo ko Mallan" Mai Gari Yayi Murmushi Yace "Banida Hurumin Haka har Sai Yarinya ta amince" Ya kalli Tasneem Yace "Kin Yarda zaki bishi? Kai ta gyada dasauri Tana Murmushi, Mai Gari Yace "Shiknan mun Amince" Godiya Naeem yayi Sosai, Yayima Mai Gari da Makocin Mallan Alheri Sannan Suka kamo Hanya, Har Sun Baro Garin Wayan Naeem Yadau Ringing, Cirowa Yayi Daga Aljihu Ganin Mai Kiran Yasa Fara'ar Fuskarshi Ta gushe, Gabanshi Yayi Mumunan Faduwa...

Ummu Farheen✌🏻
           N
Aysha Gana💕
[10/15, 7:54 AM] ‪+234 813 184 5457‬: [9/13, 6:38PM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
               N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*91 to 95*

Kurama Wayan ido Yayi Harya Tsinke. Sa'ad Ya Kalleshi Yace "Wannene?" Da Lebe Ya amsa Mai, Gyada Kai Yayi kawai Ya cigaba da Driving, Sunyi Nisa Sosai Naeem ya juya Yaga Taseem tai barci, Dan Murmushi Yayi ya juya ga Sa'ad Yace "Dr ya kake ganin zanyi??" Sa'ad yace "kayi ganganci Naeem, Bai kamata kace Haka bah, Yanzu ya zakai da Mum?, kace Mata meh?"

Furzar da iska Naeem Yayi Yace "Bah yanda zanyi Sa'ad, Tasneem bata dace da zama gidan mutumin nan bah, Kai kasan bazasu bari taje makaranta bah sai aikace aikace kawai" Sa'ad Yace "To Yanzu Ya kakeso ayi?", Naeem Yace "Zance ma Mum Kawai na maida ita, Duk Sanda Naji zasuzo sai ka taimaka min Nadawo da ita gidanka" Gyada kai kawai Sa'ad Yayi Baice Komai bah Har Suka Isa Gidan Naeem..

Dakanshi Ya dauketa Yakaita dakinta, Mai Gadi yasamu Yace Ya lura da ita zaije Office, Yace tho suka Tafi tareda Sa'ad...

Yana Office Mum ta kara kiranshi, Ya Dauka Gabanshi na faduwa, Mum Tace "Wato Bakajin Magana koh Son??" Da Karfin Hali Yace "Mum mai nayi kuma??" Oh Bakasan meh kayi bah koh??, Dan Bakajin Magana na Nace ka mayar da Yarinyan nan Anma kaqi" Yace "Mum na Mayar da ita Tun Jiya" Na kaita kauyensu beleive me mum" Tai Shiru Sannan Tace "Are You Sure?" yace "Yes mum" Tace Shiknan zamuyi magana anjima ina Hanyan Zuwa Gida Kasan Yanzu Yanma neh anan" Yace Ok mum Safe Trip..


Tunani Ya Hanashi Sukuni yanda zai bulloma Alamarin Har Lokacin Tashi Yayi, Sun Hadu da Sa'ad a Parking Space zashi Gida, Naeem Ya karasa wajanshi Yace "pls dr i need help" Sa'ad Yace "Meya Faru??" Pls Inaso ne Kasamo min Meh aiki dazata Rinka kula min Da Tasneem, Sa'ad Yace "Ok Zanyi ma madam magana tasamo mah" Naeem Yayi Murmushi Yace "Thank You Dr" Sukai musabaha Kowa yahau Motanshi..

Take away Ya tsaya ya musu Sannan Ya Karasa Gidan, Yauma A Benchn Mai Gadi ya ganta sai Kyalkyale dariya Take, Yayi Parking Ta nufoshi Dasauri Tana Murmushi, Yana Fitowa Ta rungumeshi Tace "Ya Naeem Meyasa kakeso ka maidani gurin su Iya" Yayi Murmushi Tana Shafa Kanta Yace "Nayi neh Saboda Susan kina Wajena" Batace komai bah Ya kama Hannunta Suka Shiga Ciki, Saida Sukaci Suka koshi Sannan Yace "Gobe Zamuje nasaki a makaranta" Murmushi tai Dimple dinta Ya lotsa Tace "Allah!" Shima Murmushi Yayi Yace "Eh Mana, Sai Nasaki Primary 6 koh kuma kiyi Common Entrance Kawai kije Js1", Murmushi Tai tace "Nagode Ya Naeem" Baice Komai Bah Ya Mike zai shiga Dakinshi..

Kiranshi Tai a hankali Ya juyo Yace "Ya dai?" Rau Rau Tai da ido Tace "ya Naeem Baka kaini Yawo" Murmushi Yayi Yace "Oh! Kullum kinfiso mu rinka zuwa Yawo??" Kai Ta Gyada mai Yace "Shikan Barinyi Wanka Koh" Tsale Ta Hau Yi Tana Dariya "Dan Dariya Yayi Ya Shige Dakinshi"..

Fita tai dagudu Ta samu Baba mai Gadi Suka tafa Tace "Yau Ya Naeem zai kaini Yawo" Yayi Dariya Yace "Iyeh kinji Dadi" Cikeda Fara'a Tace "Har Gobe zai sani a makaranta" Baba Mai Gadi Yace "Lallai Tasneem din Yayanta, To Allah ya Sanya Alheri" Ta koma Ciki dagudu, Falo ta zauna Sai Murmushi take Ita kadai, Harya fito, Ta mike Dasauri Tace "Mu Tafi koh", Kai ta Gyada Ya kama mata Hannu Har Mota, Baba Mai Gadi ya bude Musu Gate Suka Fita, Park Ya fara Kaita, Sai Tsalle tsalle take tana Dariya, Ya nuna Mata Abubuwa dayawa, Sunyi Yawo Sosai Tahau Chan Tahau Chan Sai Dariya Take Cikeda Nishadi...

Dakyar Ta yarda Suka Samu guri suka Zauna, Ice Cream Ya Siya mata da cake shi kuma fayrouz, Tanasha Tanamai Hira Yana Dariya, Phone Dinshi ne Yahau Ringing, Ya kalleta yace "Ina Zuwa barin Dauki waya, Karkije ko ina" Kai ta gyada mai ya Mike yabar wajan, Cigaba dashan ice cream dinta tai, Kamar ance ta Kalli Gefenta, Ta hango Wannan Saurayin nan Da take kira Bature, Yana Tsaye Hannunshi rike da power horse, Kauda Kai tai ganin Bai Ganta bah, Kara dagowa tai karo na Biyu Suka Hada ido, Murguda Mai baki tai Tamai Gwalo, Ga Mamakinta Sai Taga Shima Ya murguda mata baki Kamar yanda tamai Ya mata Gwalo, Kyalkyalewa da dariya tai, Daidai nan Naeem Yadawo, Yace lapia meyfaru kiketa dariya Haka?? Ta juya Tareda Mai nuni Inda Taga saurayin Anma Taga wayam Bashi, Mikewa Dasauri tai tana waige Waige, Yace "wai menene?" Tace "Wannan Baturen neh" Dan tsaki yaja Yace Tashi mutafi, inaso naga waye Baturen Nan sannan Na gargadeshi Ya daina kallanki banso..

Toh Pha *Shin Wanene Wanda Tasneem Take Kira Bature??* Ku Cigaba da Binmu Sannu a hankali..

Munayi ma Masoyan mu Barka da sallah, Dafatan Anyi Sallah Lapia. Allah Ya maimaita mana Ameen...Sannan Muna Baku Hakuri na Rashin post Kwana biyu Hakan ya Faru ne Bisa Wasu Dalilai but Insha Allahu Zamu cigaba..

Ummu Farheen✌🏻

  N
Aysha Gana💕

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
              N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*96 to 100*

Haka Suka Koma Gida Tasneem Cikeda Nishadi Gobe Za'a Sata a Makaranta...

Da sassafe Ta tashi Tai Wanka, Wani Riga da Skirt na atampha Tasa Sai dan karamin baby hijab dinta, Falo ta fito ta zauna tana jiranshi, Saida Ya shirya Tsaf Ya Fito dan Yau yana Azumi, Ta gaidashi Ya amsa, Yace "Mutafi Koh??" Kai ta gyada mai Ya kama Hannunta Suka Fito, Wani Makaranta mai kyau da tsada Naeem Ya kaita Anmata Registration da komai, Sun Mata Exams Daga Karshe Sukace Ya Bari dama Saturday za'ayi Common Entrance Sai tai Kawai, Yayi Musu Godiya Suka karasa Asibiti..

Office dinshi ya bude Yace ta shiga zaije Ward round, Ba musu ta Shiga ta zauna, Chan sai ga Breakfast ankawo mata, Saida ta cika cikinta Sannan Ta Sa Hannu a Gefen Skirt dinta ta ciro Papern datake Rubutu a Ciki tadau Biro ta Cigaba..

Saida Ya Gama Tsaf Sannan Ya dawo Office din tareda Wata mata Yar dattijuwa, Naeem Yace "Tasneem" Tace Naam Yaya, Yace "Ga Mai aiki daga Yanxu ita zata Rinka miki girki Tana miki komai, Murmushi tai ta kalli Matan, Yace "Kuzo muje Namaida mu gida Nadawo" Bah musu ta tashi suka Fito, Gida ya kaisu Ya fita ya Sayo komai na Bangare na kayan abinci Ya kawo Sannan Ya koma office..

Tasneem Ta kalli Dattijuwan Tace "Sunana Tasneem ke Menene Sunanki?" Matar tai Murmushi Tace "Sunana Laraba" Murmushi Tasneem Tai Tace "Kina kama da Iya zan rinka kiranki Mama" Tai dan Murmushi Tace "Tho nagode" Tasneem Ta taso Tazo kusada ita tace "Inane Gidanki??" Kema kinada Yaya?? Dan Murmushi Matan tai Ta Girgiza kai kawai, Tace "Tashi ki nuna min gidan" Tasneem Ta mike Ta nuna mata ko ina...

Haka Suka Cigaba da Zama da sabuwar Mai aikinsu, Tasneem ta Saba da ita sosai Sai Shagwaba da sangarta data Kara, Naeem Naji da ita Sosai, Yau Saturday Da Wuri Mama Laraba ta tashi Tasneem tai wanka, Abinci ta hada mata Taci Sannan tadauko mata Kaya, Turo baki Tasneem tai ta bata rai, Laraba Tace "Menene?" Tasneem Tace "Ni banason wannan kayan" Laraba Tace "Tho Wanne?" Wanda ta cire Ta nuna mata, Laraba tace "Tho kinga Fah sunyi Dati Tasneem kiyi Hakuri Kisa Wannan" Maqe kafada Tai Tana Turo baki...

Naeem ne Yayi Sallama Ya shigo dakin Cikin Shadda Brown, Sai zuba kamshi yake, Ya Gaida laraba Ta amsa Fuska a sake, Yace "Lapia Meya Faru Har yanzu My love bata Shirya bah" Laraba Ta fadamai Yanda Sukai, Ya tsuguna Ya kamo Kafadanta Yace "Kiyi Hakuri kisa Wannan, Kinga Wannan Yayi datti, Na miki alkawari idan kikayi kokari zan Sai miki Ice Cream da cake da chocolate, Washe baki tao Tadau Kayan ta fara sawa, Ya mike yace "Mama Laraba Idan Ta gama ta fito ina jiranta a Falo" Bai jira mai zatace ba yabar dakin...

Sunje Makarantan Saida Ya tabbatar Sun Fara Exams din Sannan Ya Tafi Asibiti, Sai Yanma Suka Gama duk Ta gaji Ya Dawo Ya dauketa Suka Tafi Gida, Suna Shiga Falo Direct Dinning Ta nufa ta zauna Ta shiga Cin Abinci, Dakinshi Ya Nufa ya Kwanta dan Yau baijin Dadi, Tasneem Na gama cin Abinci Mama Laraba tace "Oya Tashi muje Kiyi Wanka, Ta Turo Baki tace "Ni bazanyi Wanka bah" Mama laraba tace "Kinaso ace miki kazama neh?" Duk wanda beyi wanka ba Wari yakeyi...

Turo baki Tasneem tai tace "Ni To bake Zakimin Wanka bah, Sai kita Gurjeni, Ni Yaya zaimin Yau ko ki bari nayi dakaina ai na iya" Mama laraba Ta Zaro ido Tace "Naeem ya miki wanka??" Gyada kai tai, Mama Laraba Tace "Namiji bayama Mace wanka sai idan ya aureta, Bah Kyau kinji??" Kai Tasneem ta Gyada Dakyar ta shawo kanta Tai Mata Wankan, Ana mata Tasa Kaya ta Nufi dakin Naeem, Ganin Watan Dakin a kashe yasa Ta Shiga Tana Kiranshi a hankali, Tuntube Tayi da wani abu Ta fada Kan gadon, Jitai ta Fada kan mutum Yace Wayyo Jama'a ta Kasheni...

Ummu Farheen✌🏻
            N
Aysha Gana💕
[10/15, 8:01 AM] ‪+234 813 184 5457‬: [9/16, 9:53PM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
              N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*101 to 102*

Tuntube Tayi da wani abu ta fada kam gadon, jitai ta fada kan mutum Yace "Wayyo Jama'a ta Kasheni, Ihu Ta saki Tana kokarin Mikewa, Rikota Yayi Ya Matseta a jikinshi Yace "Its all Right nine Naeem" Ajiyan Zuciya Tai Yace "Kinaso ki Kasheni koh?" Ta Turo Baki Tace "Nifah Bansan Kana nan bah" Kuma Faduwa nai, Baice Komai bah Sai ajiyan zuciya Dayake, Lamo tai a jikinshi Tace "Yaya jikinka Zafi bakada lapia ne" Yace "Banida Lapia kuma kinaso ki Karasa ni"...

Kici kicin Kwacewa Takeyi Ya matseta Yace "Ranan Monday Akwai School Sannan Banda Kula Maza Kinji?" Tho Tace a Shagwabe, Yace "Tho dagani" Ta Mike Tadan Tsunguleshi Yace Ouch! Zan kamaki, Wutan Dakin Ta kunna Tamai Gwalo ta Fita, Mama Laraba tasamu Tace "Mama Laraba Ya Naeem Bashida Lapia" Laraba Tace "Inna Lillahi Ya jikin Nashi?" Turo baki tai Tace Oho Nima Bansani bah"...

Kicin ta shiga Tafara Kiciniyan Hada Mai Abinci, Tasneem tace "Mama Laraba meh zakiyi?" Tace "Zan dan daurama Naeem wani abu ne Yasamu Yaci" Turo Baki Tasneem Tai Tace "Uunmm" Ta Fita...

Cikin Minti kadan ta hada Pepper soup din kayan ciki da Zobo, A tray ta daura komai Ta fito, Tasneem tasamu a kasa gefen Kitchen din tana wasa da Teddy dinta, Tace "Tasneem Taso ki kaima Yayanki" Ta turo baki tace "Mama Laraba bakiga Yar Tsanata Tanajin Barci baneh, Ki Bari idan Tai barci", Mama Laraba Tace "kinga Fa baida lapia baici komai Yi hakuri Kinji, Kawota na Kwantar miki da ita kije ki dawo"...

Mikewa tai ta aje Teddyn akan Kujera Tace "Tho Mama Laraba ki Lulubemin ita Kinga fah tanajin Sanyi" Tho Mama laraba Tace Ta mika mata Trayn, Kokarin Zubarwa Take Tace "Kin Rike dakyau kinji?" Tho Tace Ta nufi dakin, Saida ta aje a kasa ta bude kofan Sannan ta dauka ta shiga dashi..

Zaune ta Sameshi gefen Gado daure da Towel Yana Tsane Ruwan kanshi, Daga Gani Yanzu ya fito daga Wanka, Sakin Trayn Tai ta Kwalla Ihu, Fitowa tai dagudu Ta rungune Mama Laraba tana Muna Mata dakin, A Rude Mama Laraba Tace "Lapia Tasneem Menene?" Dakin Ta Cigaba da Nuna Mata tana Kara shigewa Jikinta, Naeem Koh Gabanshi ne Fadi Jalabiya ya zura ya fito a rude, Mama laraba Tace "Lapia??" Naeem Yace "Bansani bah Tana Shigowa ta Yarda Trayn ta Fito Tana Ihu"..

Tsugunawa Yayi Kusada Ita Ta matsa Dasauri tana Kokarin Guduwa, Ya Kamota Ta kara kwalla ihu, Ya Riketa Sosai Yace "Tasneem menene" Kokarin kwacewa ta cigaba dayi, Mama Laraba Tace "Tho zo nan ki fadamin" Bah musu ta koma Gurin Mama Laraba, Tace "Tho Fadamin menene?" Matsar Kwalla ta fara tana Kallan Ya Naeem Tace "Koba Ya Naeem Dan Iska b..., Bata karashe ba Mama laraba ta rufe mata baki tace "Kar na sake ji"

Kunya ne ya Kama Naeem Yadan Kalleta Yace "Menayi?" Ta Turo baki a shagwabe tace "Koba kai bane Bakada kaya sai zani" Dariya Naeem ya Guntse Ya mike, Mama Laraba Tace "Kedai Wallahi Allah Ya shirye ki!" Bah Nace ki rinka sallama in zaki shiga dakin mutum bah??" Tace "Tho fah Mama Laraba nayi" Anma ai cewa nai sai ance ki shiga koh??" Batace komai bah Ta turo baki ta koma Tadau Teddynta Ta fita Wajan mai gadi...

Mama Laraba Tace "Ashe bakaji dadi bah?" Yadan Sosa Keya Yace "Eh Anma Alhamdulillah nasamu Sauki, Tace "Tho Allah ya kara sauki, Yace Ameen tareda komawa  dakinshi...

Haka suka yini Tasneem sai kumbure kumbure take taki ta kula kowa dakyar Naeem Ya shawo kanta suka fita yayi mata shopping Sosai sai dadi takeji suka dawo gida...

Exams ya fito Tasneem tayi kokari sosai, Har ya mata registration an dinka mata uniform Ranan monday Zata fara zuwa, Dadi gurin Tasneem ba'a magana, da Tsalle ta samu baba mai gadi tana fadamai, Ya tayata murna sosai Da yi mata addua...

Siyaiyan Makaranta Ya mata tun daga kan socks, takalmi, jaka, litattafai dadai sauransu, Suna dawowa ta nunama Mama Laraba tai Murna sosai tareda sa Alheri..

Ana Gobe zata Fara zuwa Makaranta, Ta Shiga dakin Naeem da Sallama, Kwance ta sameshi saman gado yayi ruf da ciki yana Danna Laptop dinshi, Amsa Sallaman Yayi batareda ya kalleta bah, Ta Hayo gadon ta aje litattafan a gabanshi, Kwanciya tai ta daura kanta a bayanshi tace "Ya Naeem baka rubutamin suna bah" Idonshi na Kan Laptop din Yace "Oh! my love Case!, Kinzo ki hanani aiki koh?" Ta Turo baki tace "Ya Naeem ka rubuta min sai in tafi" Yadanyi Shiru yace "Tho Ki Bari in Gama Kinji my love?"...

Kai ta gyada Tayi lamo a bayanshi, Chan ta Sarkalo hannunta na dama a wuyanshi tace "Ya Naeem kai menene sunan babanka??" Dan Murmushi Yayi Yace "Sunan babana Umar" Tai Dariya Tace "Sunan Abokin Ya Tasiu" Ta kara kallanshi tace "Mamanka fah?" Yace "My Love kinaso ki hanani Aiki koh??" Ta turo baki Tace "Tho Ina mamanka da Babanka??" Koh Kai bakada Mama da Baba?? Zaro Ido yayi...


Ummu Farheen✌🏻
             N
Aysha Gana💕



[10/9, 7:44 PM] 🍹🍬🛍💍Salma🍷💍🛍🍬: [9/17, 10:18PM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
             N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*103 to 104*

Ta Kara Kallanshi tace "Mamanka fah?" Yace "My love kinaso ki hanani aiki koh?" Ta Turo baki Tace "Tho ina mamanka da Babanka??" Koh kai bakada Mama da Baba?? Zaro ido Yayi Yace "My Love bakin nan naki koh?" Mikewa tai tana kumbure kumbure tabar dakin, Dan Dariya Yayi Yadau biro ya rurubuta mata sunanta Ya Fita Ya aje mata kan Dinning...

Da Sassafe Ta tashi Tashiga wanka, Mama Laraba ta Rike baki tace "Oh Yau Tasneem wanka ake kamin ace Lallai Yau Yan gidan nan Zasusan za'a Fara zuwa makaranta" Tana Fitowa tadauko Uniform din ta aje akan gado, Fita tai Tasamu Mama Laraba a Kitchen tana kici kicin daura Breakfast, Tace "Mama Laraba Kizo ki nunamin Yanda akesa Kayan Banso inyi Latti", Dan Dariya Mama Laraba tayi Tace "Tho kije Ina zuwa" Tho tace Ta Fita Anan ne Taga Litattfan Tadauka tana Turo Baki ta Nufi Dakin...

Mama Laraba ce ta shirya ta Tsaf, Riga Da Skirt ne, Blue Skirt Sai light Blue Riga, Da Dan Karamin Baby hijab Fari, Kayan Sun Matukar amsar ta, Mama Laraba Tace "Kinga Yanzu Tunda Za'a Fara Makaranta dole Zaki Fara Kitso", Batace Komai bah Ta Goya Jakanta Ta Fito, Mama Laraba Tace "Tho Kyadai Tsaya Kiyi breakfast koh?" Dai Dai nan Naeem Ya fito Cikin Suit Brown da Farin Shirt Sai Red Bod Tie, Kayan sun Amsheshi Sosai, Gashin Kanshi Sai Kyalli yake..

Bata Kalleshi ba Ta Nufi Dinning din ta zauna, Mama Laraba Tai Serving dinta ita Dashi, Kadan Tasneem Taci Ta mike, Ya Kalleta Yace "Ina Zaki?? Kyadai Jira na Gama koh?" Batace komai bah Ta dawo ta Zauna a Palour tana Turo Baki, Dan Murmushi Yayi Ya cigaba da cin Abincinshi...

Saida Ya Gama Tsaf Yama Mama Laraba Sallama Sannan Ya Kalli Tasneem Yace Muje Koh? Turo baki tai ta mike Yana tafe Tana binshi a baya Har bakin Mota, Muryan Mama Laraba Taji Tana Cewa "Tasneem ga food flask dinki kin Manta, Ta Karaso Ta mika Mata Tace "Allah Ya kiyaye a dawo lapia" Ameen Tace Ta shiga suka kama hanya...

A Hanya bah Wanda Yacema Wani Har Suka kusa School din, Kallanta Yadanyi Yayi Murmushi Sannan Yace "My Love Fushi kikeyi dani??" Batace komai ba Ta Turo baki ta Maida Kallanta ga Titi, Dariya Yadanyi mara Sauti Yace "Tho Am Sorry kinji My Love, Bazan Kara Bah and Na miki alkawari kina Dawowa zan Fada miki kinji??...

Batace komai bah Still har suka kai Makarantan, Fita Tai Shima Ya fito Suka Shiga Cikin School din, Saida Aka bata Class Ya Rakata Har Ajin Yaga Ta Zauna Sannan ya Mata Bye Bye, Ga Mamakinshi Yaga Itama Ta daga mai hannu Harda Murmushi, Yana Tafiya Wata dake Kusada Kujeranta tace "Kema Yau kikazo??" Kai Tasneem ta gyada Itama Tace "Nima Yau nazo"...

Sunana Yusra Kefa? Tasneem Tace "Nikuma Tasneem" Bell akai ringing na Fita Acembley Suka Fita Tare, Ranan Tare Sukai Yawo itada Yusrah Ta Koya Mata Wasu abubuwa da bata Sani bah Haka Itama Tasneem Ta koya ma Yusrah...

Ana Tashi Suka Fito a Tare Har bakin Gate, Nan Tasneem Ta hango Motan Naeem, Ta kalli Yusrah tace "Ga yayana Bye sai Gobe" Yusrah Ta dago Mata Hannu Itama Tace "Nima Ga mamana Chan", Motan Ta shiga Naeem ya hade rai Yace "Har kin Fara Yin Kawaye koh?" Ganin Yanda Ya hade rai Yasa ta Tsorata Tace "Itafa ta fara min Magana", Yace Harda Maza koh? Ta Girgiza kai Dasauri tace "Aa ban Kula kowa bah" Ajiyan zuciya yayi Yace "Banaso ki kula kowanne Namiji kinji?? Har Uncles Dinku Indai bah Tambayanki Sukaiba Akan Karatu" Kai ta Gyada Sannan tace "Tho"

Ya Kura mata Ido Na kusan Minti Biyar Sannan Yace "Ina Sanki Tasneem Bana fatan Naji ko Naga Abinda zai Rabani dake, Hannunta Ya rike Ta Kalleshi Suka Hada ido yace "I Love You Ok" Murmushi Kawai Tai Batace Komai Bah, Yace My Love koh ke Bakya Sona?? Bakyaso Muyi aure Wata Rana mu haifi yara??

Dan Dariya Tai Tasa Hannu ta rufe Idonta Yayi Murmushi Yace "Bakyaso?" Tace inaso, Wani Kayataccen Murmushi ya Saki Ya Kunna Motan Suka Kama Hanya, Suna Tafiya Tana Bashi Labarin Scul, Hold Up ne Ya Rikesu Sai Shagwaba Take Ita Yunwa Takeji, Kamar Ance ta juya Tako Hango saurayin Nan Cikin Motarshi, Hada Ido sukai ya Mata Murmushi, Murguda mai Baki tai, Sai Kawai Gani Tai itama Ya murguda Mata, Gwalo Ta Sake mai, Shima Ya mata, Dariya Ta Saki dai dai sanda Hanya ta bude, Naeem Yace "Lapia?" Tace "Wannan baturen neh kemin Gwalo"..

Mamaki Fal Fuskan Naeem Yace Gwalo kuma? Ina Yake? Juyawa tai taga wayam bah kowa Ta juyo tace "Ban Ganshi bah" Baice Komai Bah Har suka iso Gida, Food Flask din kawai ta dauka ta fito Tabar Jakan, Tana Shiga Falon Dinning Ta nufa Kai Tsaye, Mama laraba dake falo tace "Tasneem bako Sallama Bare Gaisuwa kin Tafi gurin Abinci? Turo baki tai tace "Nayi fah Bakiji baneh" Abincin Ta soma Zubawa, Naeem Yayi Sallama rike da jakanta, Mama laraba tace "Oh Manya Fa an Fara zuwa makaranta, jakan kuma yayanki ne Zai Rinka dauko miki"..

Batace Komai ba sai Saka Loma take, Dan Murmushi Naeem yayi Ganin Yanda Take cin Abincin Tana Lumshe Ido Alamar Taji Yunwa, Dakinshi Ya Nufa dan Rage kayan Jikinshi...

Haka Tasneem Ta cigaba Da zuwa Makarantan ta, Shakuwa Sosai Ya shiga tsakanin Yusrah Da Tasneem, Ta fara Fahimtar Turanci Sosai, Ga Maida Hankali da Tasneem Tai Ga Karatun, Shakuwa Sosai ya Kara Shiga Tsakanin Tasneem Da Naeem, Every Week end Yakan Dauketa Suje Shopping Da Wuraren Shakatawa Sosai, A Haka har Tai Wata Shidda a Gidan Naeem, Yanzu Suna js1 Second Term...

Yau Yakama Saturday da Wuri Naeem Yatashi ya shirya cikin Shadda Golden, Sai Hula Kalar Shaddan, Kayan sun matukar Mai Kyau Ya Fito sai baza kamshi Yake, Tasneem Da mama laraba na palour Zaune Suna Kallo ya fito, Tasneem Ta mike dasauri Tace "Ya naeem Ina zaka?" Yace "Anguwa" Tace "Tho nima zani" Kai ya girgiza Yace "Aa Kiyi Hakuri bazan dadeba zan dawo kinji, Turo baki tai ta rungume Hannayenta Ta Shiga Daki dagudu Tana kuka, Mama laraba tace "Kyaleta zoka Wuce" Dan murmushi Yayi ya mata sallama ya Shiga mota Yadau hanyan Gangara Hayin Mallan...


Ummu Farheen✌🏻
   [truncated by WhatsApp]
[10/9, 7:44 PM] 🍹🍬🛍💍Salma🍷💍🛍🍬: [9/20, 7:15AM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
             N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*105 to 106*

Turo baki Tai ta Rungume Hannayenta ta shiga Daki dagudu tana kuka, mama laraba tace "Kyaleta zoka wuce" Dan Murmushi Yayi Ya Mata Sallama ya Shiga mota Yadau Hanyan Gangara Kauyen Hayin Mallan, Koda Ya Isa Direct Gidan Mai Gari ya Nufa, Saida Ya mika Gaisuwa Sannan Ya gabatar da Kanshi...

Mai Gari bai Manta Dashi bah, Sunyi Gaisuwar Mutumci Sosai, Naeem Ya gyara zama Yace "Dama nazo ne akan maganan Tasneem ko Mallan ya dawo?? Koh Yayanta" Mai Gari ya kalli Liman Suka hada ido Sannan Liman Yace "Gaskiya Mallan Bai dawo bah, Sannan Yayanta Kuma Tabbas Munji Labarin Yadawo Anma Sam Bai nememu bah, Dan Ance Ranan Da Ya dawo Ana Fadamai Cewa Kanwar ta Bace Yabar garin Yana Kuka"...

Girgiza Kai Naeem Yayi Yace "Tho Dan Allah Bah wanda Yasan Inda Yake Makaranta?? Nadai San ance Zaria Neh ABU anma Nemanshi Yanzu dakamar wuya, Domin Makaranta ce mai Girma, Mai Gari Ya Gyada Kai Yace "Hakane, Yanzu dai Ka Bari tukun Har Sai Allah Ya Kawo Mallan din", Naeem Yace "Tho bakada Waya Saina Rinka Kiranka inaji??" Mai Gari Yace "Mallan Liman Bashi Numbern ka Kwa Rinka Waya", Liman Yace "Tho Ranka Ya dade" Karanto ma Naeem numbern Yayi Yana Rubutawa, Sunyi Sallama Ya Musu Alheri Sosai Sannan Yadau Hanyan Komawa...

Direct Gidan Sa'ad Ya nufa, da Fara Ya Tarbeshi, Saida Suka Natsu Sannan Naeem Ya Fadamai duk Yanda sukai da Maigari, Sa'ad Yace "Hakan ma Yayi anma Naeem Yazakai da Mum dakacema Kamaida Ita Gida? Ina Tsoron abinda zaije yadawo fah", Tabe Baki Naeem Yayi Yace "ah dnt worry babu abinda zaije yadawo insha Allah,"...

Hira Suka dan Taba Daga Bisani Naeem Yamai Sallama Ya Dau Hanyan Gida, A Haraban Gidan Yaga Tasneem Kwance Ruf da Ciki a kan dan karamin carpet Tana Rubutu, Ya Karasa Da Murmushi Yace "My Love Nadawo Assignment kikeyi neh?" Turo baki tai Ta mike ta zauna Ta juya Baya, Sam Naeem Ya manta Fushi Take, Rarrafawa Yayi yadawo gabanta ya riko Hannunta Yace "Haba my love banaso kina Fushi dani am sorry kinji?", Turo Baki tai idonta Ya ciko da kwalla Tace "Koba Kai Baneh Kaki Zuwa dani", Naeem Yace "Am Sorry Inda Naje bai kamata Naje Dake bah, But kibari next week end sai muje Yawo koh??" Kai ta Gyada Tana Murmushi...

Littafin Hanunta Ya Amsa Yace "What are you doing??" Tai Murmushi tace "Assignment" Yace "Can i help you wit it??" Kai ta Gyada, Zama Ya Gyara Ya Shiga Solving mata Maths din Yanayi Yana Bata Tayi Yagani, Saida Ya Tabbatar ta iya Sannan Sukai Assignment din"...

Ranan Monday da Safe Tasneem Ta fito Shirye Ciki kayan Makarantan Tah, Dinning ta Zauna Ta Fara Breakfast, Shiru bah Naeem, Ta mike Tai knocking a Dakin ta Shiga Kai Tsaye, Kwance Tasameshi Yana Barci Hankalinshi Kwance, Hannu ta daga Zata Kai mai duka Sai kuma Tafasa Dabara ya fado mata, Toilet ta shiga Ta debo Ruwa Ta Yayyafa Mai a Fuska, Zumbur Ya Mike dan Ya matukar tsorata, Ganin Yanda Yayi Yasa Tasneem Kyalkyalewa Da dariya..

Hade Rai Yayi ya kira Sunanta a hankali, Ta Kalleshi Tana Cigaba da dariyan, Yace "My love why this?" Ta Turo baki a Shagawabe Tace "Tho bah kai baneh Kaki Tashi kai Breakfast ta kaini School", Mamaki karara a fuskarshi Yace "School kuma?, Shi Ali Drivern menene anfanin Sa??" Ta Bata Fuska Tana Bubugawa a kasa Tace "Nidai kai nakeso ka kaini" Baice Mata komai bah yadau Bargo ya lullube daga Kai har kafa..

Zaro ido tai da Mamaki, Hannu tasa Tana kokarin Janye bargon anma ta kasa, Dakyar Allah Yabata Sa'a Ta Janye Ta Yar, "Ohhh! My Love Rigima, pls kibari nai Barci ga Ali kice Yakaiki I promise you idan kunyi closing ni zanzo nadaukeki" Turo Baki Tai Ta Fita tana gungunai"...

A Hanya Ali Driver Yace "Yaukam Tasneem kinyi Latti" Ta turo baki Tace "Tho ba Yaya Nace Yakaini ba Yaqi", Murmushi Ali Yayi yace "Tho bagani bah" Batace Mai Komai Bah ta maida Kallanta ga Titi, Ido Suka hada da Baturen nan Cikin Hadaden Range Rovern shi Baki, Sanye Yake da Suit Fari kar, Gashin Shi luf Luf Kamar na Yan india...

Murmushi Ya mata Ta Galla Mai Harara, Maida Dubanshi Yayi kan Titi Yana Murmushi ahankali, Ta Turo Baki Tareda tsaki, Ali Driver Yace "Duk Rashin Kaiki Makarantan neh Haka??, Batace Komai Bah ta Kara kallan Window, Ko Alamarshi Batagani bah, Sai bin Motoci take da Kallo har Suka Kai Makaranta...

Yusrah ta Fara cin Karo da Ita a Bakin Gate din makarantan, Murmushi Sukaima Juna Suka Shiga Cikin Makarantan, Saida Aka Tashi Break Yusrah Tace "Kullum Inaba Ummana Labarinki Tace tanaso Taganki" Murmushi Tasneem Tai Ta dauko joter a Jakanta Tace "Ki Rubuta min Address dinku sai Nace Yaya Naeem ko Ali Ya kawoni" Bah Musu Ta rubuta mata Tasa a jaka...

Kamar Yanda Naeem Ya Mata alkwari Ana tashi Ta fito taga motanshi Yayi parking yana jiranta, Dan Murmushi tai ta karasa ta Shiga, Ya Kalleta yana murmushi Yace "My Love rigima, Shine kika  Tafi Bako Sallama koh?" Batace Komai ba Ya Ja motan suka Dau Hanyan gida...

Haka Rayuwa yacigaba da tafiya, Gari ya waye, Rana ta Haska, Dare Yayi Kullum Rayuwa Sai kara tafiya Take, Yanzu Tasneem Tana Js2 Second term, Ta kara Girma Tayi Tsawo, Yanzu Tana shekara Sha Uku, Naeem Yakan Kira liman yaji Labarin ko akwai wani Labari gameda Tasiu ko Mallan, Amma Shiru...

Yau Kamar Kullum da Sassafe Ta shirya Tana Breakfast a kan Dinning, Naeem Ya fito Dasauri Yana kokarin Fita, Ta Kalleshi tace morning Ya Naeem! Sai a Sannan ya Lura da ita, Yayi Murmushi Yace "Oh Sorry My love Inada Emergency Theater ne a Asibiti, Tai murmushi Tace "Ok saika dawo" To Kawai Yace ya fita Dasauri, Mama laraba ta fito dauke da Breakfast din Naeem, Tasneem Tace "Ai Ya Tafi wai Yana sauri" Ta mike Tace "Nima Natafi, Mama laraba tace "Adawo Lapia"...

Tana Dawowa Ta Shiga Falon Dasallama, Decorating Falon Akai Ko Ina, Sai Wani hadaddun Cakes Tagani Guda Uku Akan Center Table, Yanda akai Decorating Falon Da cake din Ya matukar Burgeta, Karasawa tai Tana Kallan Cake Din, Daya an Rubuta "Tasneem is 13" Daya kuma An Rubuta "My Love is 13" Sai dayan aka Rubuta "Naeem and Tasneem" Idonta taji an Rufe Zatai magana Naeem yakai bakinshi Daidai saitin Kunnenta Yace Shhhh!..

Ummu Farheen✌🏻
  [truncated by WhatsApp]
[10/9, 7:44 PM] 🍹🍬🛍💍Salma🍷💍🛍🍬: [9/20, 4:00PM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
               N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*107 to 108*

Idonta Taji an Rufe Zatai Magana Naeem Yakai bakinshi Daidai Saitin Kunnenta Yace "Shhh", Gyalle Yasa Ya Rufemata Ido, Sannan Ya Rike Hannunta Har Dakinta, Idonta Ya Bude, Dakin Tabi da Kallo, Komai na dakin an chanza, Komai Pink akasa, Sai Manya Manyan Teddys da Aka Sa A Gefe Gefen Gadon, Dagudu Ta karasa Ta Dauki Daya Ta Rungume, Bangon Dakin Duk Hotunan ta ne Da Batasan ma Duk Sanda aka dauketa bah...

Shagala sai da kallan dakin Tana Murmushi Zuciyarta Fari Kar, Juyowa tai ta Kalleshi Ta zuba mai Narkakun Idanunta Tace "Ya Naeem duk Nawa??" Murmushi Yayi Ya Gyada Mata Kai Sannan Yace "Happy Birthday", Dan Dariya Tai Tace "Ya Naeem Ya akai Kasan Yau Birthday nah??" Yace "Keh Kika Fadamin Ranan Kikace Yaya Tasiu Yace an Haifeki 12 august, Ta Gyada Kai Hawaye Suka Gangaro mata, Karasawa Yayi Ya Rike hannunta Yana Girgiza Mata Kai, Yace "Banason Kukan nan fah" Ta kara Fashewa da kuka Ta Rungumeshi Tace "Ya Naeem Dan Allah Kace Ya Tasiu Ya dawo, I Miss Him" ...

Baice komai bah Ya Rike Hannunta Suka Fito, Mama Laraba Tagani Tsaye a Falo Tana Mata Murmushi, Kayane na Alfarma A jinkinta Sai Hijab kalan Kayan, Mama Laraba Tace "Happy Birthday Tasneem" Murmushi Tai Ta Share Hawayen Idonta Ta Karasa da gudu ta Rungume Mama Laraba..

Murmushi Naeem Yayi yace "Kije Kiyi Wanka Kizo Kinji" Bah Musu Sukai dakinta itada Mama Laraba, Tasneem ta shagaltu da kallan dakin Dakyar Tai Wanka Tasa Pink Gown da Black Turban, Mama Laraba Ta Shafa Mata Yar powder a Fuska, Kayan Sun Matukar amsarta, Naeem Na zaune a Falo Suka Fito, Murmushi Yayi Yace "Kinyi Kyau My Love", Dan Karamin Wuka Ya soka a Cake din Tsakiya Wanda aka Rubuta "My Love is 13" Waka Ya hau Mata Yana Tafi ahankali, Mama laraba ma Tafin take tana Murmushi, Dariya Tasneem keyi Naeem Yace "1!, 2!!, 3!!, " Cake din ta Yanka Naeem Ya Dauka Yace "Haaa! Bude Baki, Baki ta bude Har yakai mata Bakin Ya kawar ya dangwala mata a Hanci," Dariya ta saka, Itama Mama laraba dariya Tayi...

Yanka Tasneem tai Taba Mama Laraba a baki, Itama Taci, Naeem Ya langwabar dakai Yace "Nifah" Tace "Banda Kai" Yace Shiknan, Ya Mike Zaibar Wajan, Tace "Tho Sorry Yaya, Daukan Kato Tai Ta turamai a baki tana dariya, Dakyar ya iya Cinyewa, Yace "Keko zakisani"...

Wani Dan karamin Zobe na zinari Ya ciro Yace "Muga Hannunki, Hannu Ta Mika Mai Yasa Mata Tace "Woaw Ya Naeem Yanada Kyau", Ya Dago Suka hada Ido Yace "No matter What appstricle karki Yarda Wannan Zoben Ki cire Kinji??, Kai ta Gyada tana kallanshi, Murmushi Ya mata yace "I Love You Ok," Nan ma Ta gyada kai, Sunkuyar dakai yayi Yana dan murmushi Ga Mamakinshi Yaji tace "I Love You" Dagowa Yayi dasauri Tareda zaro ido Yace "My Love What did you just Say??" Murmushi tai ta sake maimaita wa, Ganin batasan ma'anarshi ba tadai fada ne yasa yace "Ku Muje Koh" Car Key yadauka Tace "Ina Zamu Ya Naeem?" Yace "Saidaku zanyi", Bai jira mai zatace bah ya Fita daga falon...

Gyalle Mama Laraba ta Dauko Mata suka Fita, Mama laraba na Baya tasneem nagaba, Park Yakaisu, Tasneem Ta juya ta kalleshi Tana Murmushi, Sun Zagaya wurare sosai, Sunyi Ciye Ciye iri iri, Sannan suka Shiga Kasuwa, Shoping ya mata Sosai Itada Mama Laraba, Bah Karamin murna Tasneem Tai bah, haka ta dawo gida cikeda farinciki..

Tasneem Ana shirye Shiryen Exams din Third term, Karatu Take Sosai, Naeem Kan Koya mata Wasu abubuwa dayawa Dabata Ganeh bah, Dakyar ya yarda Ali mai gadi Ya kaita Gidansu Yusrah, Taji Dadin Yanda Umman Yusrah Ta Karbeta, Kyaututuka masu yawa ta bata Sukai Sallama ta dawo Gida...

Cikin Ikon Allah Tasneem Sukai Exams Allah Ya bata sa'a Taxo na Biyu, Ranan da aka basu Hutu, Dagudu ta Shiga Dakin naeem yana Kwance yana Browsing Wani Sabon magani Daya fito, Ta shigo Tace "Ya Naeem Guest What?" Yace "wht?" Tace "Nayi 2nd Position Ta mika mai Report sheet din, Dubawa yake da murmushi dauke a fuskanshi Yace "Woaw My Love Congrats!" Tel Mie me kikeso??" Shiru tai tana tunani chan tace "Ya Naeem Zaka kaini Makka??" Sakin baki yayi Yana kallanta...

Ta Matso Tace "Ni Makka nakeso naje", Yace "Zan kaiki My Love anma ba yanzu bah" Ta turo baki tace "Sai yaushe?" Yace "Sai kin Gama Ss3 Munyi aure Kinji?" Hannu tasa Ta rufe ido Ta fita dagudu Tana dariya, Shima dariyan Yayi yace "I Love uh my love"...

Dogon Hutu aka basu Tasneem dan Haka suna Gida Bah Zuwa Koh ina, Sau biyu Yusrah tazo Gidan, Naeem yasamo mata Mai koya mata karatun islamiya kuma tana fahimta sosai...

Yau Da Wuri Naeem Zai Fita saboda Theater Kusan hudu da sukedashi, Dakin tasneem Ya Leka Yaga Tana barci, Ya shiga ya Kura Mata ido, Sam yau baisan meyasa gabanshi ke Faduwa bah, Zuciyarshi Sai rayo mai sunan tasneem Take, Tsugunawa Yayi Daidai saitin Fuskanta ya tofa mata adduoi, Gashin kanta ya shafa yace "I Love uh My love" Ya rintse ido ya bude ahankali Yace "Insha Allah you will be my Wife" Murmushi yayi ya mike Yabar Dakin Gabanshi nacigaba da Faduwa...

Mama Laraba Da Tasneem duk basusan ya fita bah, Suna Xaune Wuraren Sha biyu na Rana Suna Kallo a falo tasneem Sai Tambaya takema Mama laraba Sukaji Sallama, Wata Mata ce Ta Shigo Kallo daya zaka mata kaga tsantsar kamarta da Naeem, Idonta Sanye da medicated Glass, Yamutse Fuska Tai tace "Kufah?? What are you doing in this House??"...

Mama laraba ta Kalli Tasneem Suka hada ido tace "Kufa nake saurare" Mama laraba tace "Aiki Nakeyi a Gidan" Ta kalli Tasneem Tace "Keh kuma fah?" Tasneem Tace Ni Ya Naeem ne yakawoni" Hajiya tace "Oh! Dama bai Maidake bah koh??" To Maza Ku Tattara kayanku kubar gidan nan ko Yanxu na Kira muku yan sanda, Mama Laraba Najin haka ta mike dasauri...

Binta Tasneem Tai, Har daki hajiya ta biyosu tanata Balbala Musu Masifa, Sai zaginsu take, Kwadayaiyu, Talakawa, Mama laraba ta hadama Tasneem kayanta a akwati Itama ta hada nata, Har Bakin gate ta Rakasu da Zagi da ihu,  Tasneem Sai Kuka take Tana juyawa tana Kallan Gidan, Saida Taga sunyi Nisa da Gidan Sannan Ta dawo Tana Cigaba da balbala Masifa....

*Tho Fah! Ya Zata Kaya Idan Naeem yadawo bah Tasneem*~Ku Biyomu dan jin yanda zata Kaya~

Ummu Farheen✌🏻
   [truncated by WhatsApp]
[10/9, 9:55 PM] 🍹🍬🛍💍Salma🍷💍🛍🍬: [9/23, 7:21AM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
                N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*109 to 110*

Tafiya suke batare da sunsan inda suka nufa bah, Saida sukai Tafiya mai nisah suka bar anguwan gaba daya, Tasneem kukanta Take Hannunta Rike dana Mama Laraba, Gefen Wani Masallaci suka samu suka zauna, Mama Laraba Ta kalli Tasneem Tace "Kidaina Kuka Tasneem Allah Yana Tare damu", Kai Kawai Tasneem Ta gyada Tana Cigaba da matsar kwalla...

Har Wuraren La'asar suna Wajan a zaune, Ga Yunwa Daya Addabi Tasneem, Mama Laraba Ta lura, Wani Mutumi ne Yazo mai Bude Masallacin Dake Kusadasu, Ta mike dasauri suka Gaisa, Tace "Dan Allah Mallan Taimako muke nema Mu baqi ne Kudine Ya Katse Mana", Mutumin Yace "Tho ku zauna idan Anyi Sallah za'a nema muku taimako" Godiya Sosai Mama Laraba Tai tadawo inda Tasneem Take Itama Ta zauna...

Bayan an Kira Sallah, Sukai Alwala Mama Laraba ta Shinfida Musu Zaninta Sukai Sallah, Taimako Aka Naima Musu Cikin Ikon Allah Suka Samu Dari Biyar, Mutumin Yakawo Musu Mama Laraba Tai Godiya Sosai Sannan Ta kalli Tasneem Tace "Yunwa Kikeji koh?" Kai Ta gyada Alamar Eh, Tace "Ina zuwa ki zauna Kar kije ko ina kinji??" Tho Tace Mama Laraba Ta mike Ta Bar wajan zuwa naiman Abinci...

Ta Dade Kamin Tasamu Ga abincin da Tsada Duka na Dari biyar din ta Siya, Haka Suka Ci Tasneem Sai Hawaye Take, Kadan Mama Laraba Taci Tabarma Tasneem Sauran, Har Wuraren Mangariba Suna Wajan, Tasneem Tadan Kalli mama Laraba Tace "Mama Laraba Anan Zamu Xauna??" Shafa Kanta tai tace "Tasneem banida kowa Anan Garin, Ni yar jahar niger ce, Mun Rabu da mijina sannan iyayena sun koreni saboda gidanmu ba'a yaji, Shine Nadawo nan neman aiki" Gyada kai Kawai Tasneem tai, Mama Laraba Ta mike Ta dauko musu buta sukai Sallan Magriba Sannan Tace "Nasan Kinajin Yunwa koh?" Kai Tasneem Ta gyada, Mama Laraba Tace "Barinje in dawo ki zauna anan kar kije koh ina Kinji??" Tho kawai tace Mama Laraba ta miki Hanyan dake Kallansu, Tun Tana hangota Har Ta daina hangota...

Duk Wanda Yazo Wucewa Saiya Kalli Tasneem kowa da abinda Yake Kitsawa A ranshi, Ganin Yarinya Kyakyawa Kaman Tasneem a irin Wajan a zaune Har kuma da Akwatin Kaya a gefe, Awa daya Awa biyu Har Uku Shiru bah Mama Laraba, Ga Dare na Tsalawa, Sahu sun dan Fara daukewa Hakan Zai Nunama Dare Ya soma Yi dan Akalla Xai kai Karfe goma na Dare, Kuka Tasneem ta Fara Ta mike Tsaye, Trolleyn Ta Fara ja Tana Kuka, Hanyan Dataga Mama Laraba ta Nufa Nan Itama ta fara bi Tana Kuka tana Kiranta ahankali, Tafiya Take Ba kakautawa, Duk wanda Yazo wucewa saiya Kalleta, Jan Trolleyn take Dakyar Tana cigaba da kuka Har wuraren Karfe Sha Daya da kusan rabi...

Ganin ba Sarki sai Allah Yasa Ta tsaya Ta fara Waige Waige, Bah kowa a Titin, Har motoci sun dauke kafa, Wata Yar Runfa ta gani da Alama na Mai kosai ne ko Waina, Ciki taja Akwatin dakyar ta ajiye, Zama tai akasa Ta hada kai da gwiwa Tana Kuka da karfi, Mama Laraba Take Kira Da Naeem Sai Tasiu, Tun Tana Kukan da Karfi Har Yakai Muryanta Ya dishe Ya daina fita, Sunan Naeem kawai Take Kira Sai Tasiu, A Hankali Harta zame barci mai nauyi ya dauketa Sai ajiyan zuciya Take Saukewa...

_Naeem Fah?_

Aiki Naeem Yake Anma hankalinshi da Zuciyarshi na gida, Kasa Theatern Yayi Wani doctor Bature dake Taimaka mai Yace Ya Cigaba Coz Shi baijin dadi, Fita Yayi Ya kira Wani Doctor Don Ya tayashi, Office dinshi Ya shiga Ya dafe Kai, Gabanshi Sai Cigaba da Faduwa Yake wannan karan Yafi na Dazu, Dakyar yasa Hannu ya dafe kirjinshi Ya Runtse ido...

Dr Sa'ad ne Yayi Knocking Ya shigo Office din, Kasa Dagowa Yayi ya kalleshi, Sa'ad Yace "Lapia Naji ance Kace Bakajin Dadi bazaka iya Theatern bah" Naeem baice Komai bah kanshi na kasa Hannunshi rike da kirjinshi...

Dasauri Sa'ad Ya karasa Kusadashi Yace "Lapia whts Wrong?" Dakyar Naeem ya bude Baki Yace "I Dnt know Gabana keta Faduwa, Zuciyata Sunan Tasneem kawai Take Kirah, Banaso Wani abu Ya faru da Tasneem am so much inlove with her" Dr Sa'ad yayi Murmushi Yace "Dnt you worry Frnd bah abinda zai Faru insha Allah, Kawai dai soyaiya ce, Kuma kasata a ranka dayawa", Zama yayi Yana dan Debe mai Kewa coz Shi Ya gama duba patients Dinshi, A dadafe Naeem Yakai Karfe Biyu a Asibitin, Mikewa yayi ya kalli Sa'ad Yace "Pls Ka kaini gida i cnt drive", Sa'ad Yace "But yakamata ka Kara duba theater din nan tukun" Girgiza Kai yayi Yace "Pls take me home" Bah Musu Sa'ad Ya mike Naeem Na binshi a baya Har Bakin Motan Suka shiga suka kama Hanya...

Sun doshi Gidan Gaban Naeem Ya cigaba da Faduwa Fiye dana da, Ya kalli Sa'ad da idonshi daya Rune Yace "Sa'ad" Ya juyo Yana kallanshi, Nuna mai kirjinshi Yayi Idonshi Cikeda kwallah, Sa'ad Yace "Oh Dr be Strong Kaifa Namiji ne, Insha Allah Bah abinda ya Faru da Tasneem dinka, Nasan muna Shiga ita zaka Fara gani", Dai Dai nan Sa'ad Yayi horn Mai gadi ya Wangale gate din duka Shiga...

Baquwar Motarda Yagani ne Yasa Gabanshi Yayi Mummunan Faduwa, Dafe Kirjin Yayi ya runtse Ido, Sa'ad Yayi Parking ya Fito ya zaga Ya budemai Shima Ya fito, Ganin Yanayinshi Yasa Ya rikemai Hannu har falon, Sunan Shiga Wazasu Gani??? Mum Zaune Tana Duba Wasu Papers, Bah Naeem kadaiba har Sa'ad saida Ya razana da ganinta, Ware ido Yayi Yace "Mum!"

Ta mike Ta hade Rai Tace "Ka Kyauta Naeem Dama Ashe Bakajin Magana nah??" Da nace Ka mayar da yarinyan Nan Ashe baka mayar da itaba Kace kamayar da Ita?? Ya Dago Ya Kalleta da runanun idonshi Yace "Am Sorry Mum but Tasneem Batada kowa ne duk Yan Uwanta Basu Ba...Rufemin baki mara Mutunci" Ai yanzu dai ya kare koh Tunda tabar gidan nan saita Kara gaba Chan, Ya dago dasauri Yace "Mum dnt Tel mie Tasneem bata gidan nan" Rai a Bace Tace "NA KORETA" Juyawa Yayi Ya kalli Sa'ad Ya maida Dubanshi Ga Mum Yace "NO! NO!! NO!! MUMMM... A Hankali Ya fadi A kasa Sumame....

Ummu Farheen✌🏻
            N
Aysha Gana💕
[10/9, 9:55 PM] 🍹🍬🛍💍Salma🍷💍🛍🍬: [9/25, 5:11PM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
+2348131845457
                N
*Aysha Gana*
+2347017251433

*111 to 112*

Ya dago dasauri Yace "Mum dnt Tel mie Tasneem bata Gidan nan" Rai a Bace Tace "NA KORETA" juyawa Yayi Ya kalli Sa'ad Ya maida dubanshi Ga Mum Yace "NO! NO!! NO!!! MUMMM...A Hankali Ya fadi Kasa Sumame, Dagudu Sa'ad Ya karasa Ya Tsuguna Kusadashi Ya Rikoshi, Mum Hankali Tace "Sa'ad do Something" Ta Fita Dasauri Takira Mai gadi Daukashi Sukai Suka Kaishi Dakinshi Suka Kwantar Dashi, Cikin Kwarewa Sa'ad Yafara Aikinshi Yasamu Ya Farfado, Mota Ya koma Yadauko Kayan Aiki, Alluran Barci Yamai, Sannan Yamai Setting Drip, Mum Dake zaune Falo Hankali a tashe Tana Ganin Sa'ad Ya fito Ta mike Tace "Sa'ad i Hope all is well, Banaso na Rasa Naeem Sanin Kanka meh Shikadai Gareni" Furzar Da iska Yayi Yace "Mum Tashinshi Kawai Zamu jira Yanzu, Mum Tace "Ban Taba Tunanin Haka Daga Naeem bah"...

Sa'ad Hardakai Za'a Hadu a rufeni koh?" Saida Nace Ya maida Yarinyan Nan Anma Yaqi, Sa'ad Ya nemi Guri Ya zauna Yace "Mum Dan Allah kiyi hakuri, Wallahi hardani akaje maidata anma da mukaje mun samu duk yan uwanta sunbar garin" Mun Dan Allah Kiyi hakuri Wallahi Naeem cant live witout Tasneem" Tsaki Mum Tai tace "Tasneem din Banza" Dole Yama cireta a ranshi" inma Wani abu tamai To Wallahi kanta xai koma" Sa'ad Baice Komai Ba Ya Mike ya koma dakin Naeem...

Har Yanzu Barci Yake, Sa'ad Yayi Maintaing Drip din Sannan Ya fito, Sallama Yama Mum Akan Zaije Yadawo, Duk Hankalinta Ya kasa Kwanciya, Waya Ta dauka Ta Soma neman Layin Alhaji, Ba'adau Lokaci Bah Ya dauka, Bayani Tamai Duk abinda Ya faru, Fada Sosai Alhaji Ya mata Yace "Karta Sake wani abu Yasaman mai Da sannan Gobe Ya Hado Kayanshi su dawo tare" Bah Musu Ta amsa Da to...

Naeem bai Farka bah Sai Wuraren Goma Na Dare, Bude ido yayi a hankali tareda karanto adduan Tashi Daga Barci, A hankali ya juya Damanshi, Mum ce Zaune Ta Shiga duniyar Tunani, Mikewa Yayi Zaune yakai Hannunshi Yakai kan Giving set ya Kashe drip din Sannan Ya mike Dakyar, Dasauri Mum ta mike Tana Mai Sannu, Baice Komai ba Ya Shige toilet din, Tana Ganin Haka ta fita dan nema mai abinda zaici, Wanka Yayi Tareda Alwala, Saida Yayi Sallah Sannan Ya fito Dakin Tasneem Ya Shiga Idonshi Cikeda Kwalla...

Ganin Dakin Yayi duk a barbaje Waldrop dinta ma a bude wasu kayan a kasa, Teddynta Yagani a Kasa Ya karasa Hawaye na Gangarowa Daga Idonshi, Dauka Yayi Ya Rungume Yana Kuka a hankali, Yakai Musan Minti goma A haka Ya mike dasauri Kamar an Tsikareshi, Fitowa Yayi yakoma Dakinshi, Makulin Mota Ya dauka Ya fito...

A falo yaci karo da mum tace "ina zaka da Daren nan?" Yadago runanun Idonshi Yace "Zanje Na duba Patients dinda Nama Theater dazu ne" Shiru Tai Sannan tace "Sai ka bari sai gobe koh?" Yace "Yanzu Wani doctor ya kirani Yace Wasu basu Farfado bah" Hararansh Tai Tace "Karya baima kyau son, Kaje duk ma inda zaka Allah Ya kiyaye"...

Hanyan Kofan Yayi Dasauri Yana kokarin Fita, Kiran Sunanshi tai a hankali ya juyo Tace "Sannan Idan Kaje Asibitin Kadauko duk wani abu naka Saboda Dad dinka Yace "Gobe dole Tare Zamu koma", Hawaye Ya gangaro daga idonshi Baice komai ba ya Fita, Motarshi ya dauka ya fita daga gidan Dagudu, Layika Layika yake bi Yana Waige Waige, Duk Inda Yaga Gungun Mutane Saiya tsaya Ya tambaya, Anma duk wanda ya tambaya Sai Yace "Bai Gansu bah"...

Har Karfe Sha daya na Dare naeem nata Yawo yana Tambaya, wani Layi Ya Shiga Dai dai Wajan Wani Shago yaga wasu Samari zaune sunata Hira, Parking Yayi Ya Fito, Wajansu ya nufa Yabasu Hannu suka gaisa, Tambayansu Yayi Kowa yace "Bai gansu bah" Daga Cikin Shagon Wani Yace "Tabbas na gansu ba Wata Yar Farar Yarinya ba Yar doguwa Kyakyawa, Da kuma wata Yar dattijuwa Wankan Tarwada" Dasauri Naeem Yace "Eh sune Dan Allah ina xan samesu?" Mutumin Yace "Dazu dai Bakin Masallacin Dake bakin Titi nagansu Anma yanzu basa Wajan" Nagode Kawai Naeem Yace Ya Shiga mota Ya nufi Masallacin, Wayam bah kowa a wajan, Har xai Tafi Ya Hango Dankwalin Tasneem, Yakarasa ya dauka Hawaye Cike a idonshi..

Yawo Sosai Naeem Yayi Har Karfe Shabiyu da rabi, Ganin Mum ta Fara nemanshi Yasa Ya nufi Gida Hankalinshi a Tashe...

*Tasneem Fah*

Barci ne Ya dauketa Bata Farka ba sai dataji wani masallaci kasada ita ana kiran sallan Asuba, Mikewa tai ta zauna Hawaye Ya gangaro Mata tunawa datai Tabar Mama Laraba da Ya Naeem dinta, Kuka ta fashe Dashi mai Tsuma Zuciya Tana nan har Mai Runfar tazo, Ganin mutum tai zaune da Akwati a gefe, Ta matsa dasauri Tace "Kefah me kike a runfa na??" Tasneem Takara Fashewa da Kuka Tace "dan Allah kiyi hakuri banga mamana ba, Shine nazo nan na kwana" Shiru Matar tai alamar rashin Fahimta, Sannan tace "Tho ina maman naki taje?" Tasneem Tace "An Koremu ne a gidan da muke shine Mamana tace zataje tasamo mana Abinci kuma bata dawoba..

Rushewa da kuka ta karayi Tana Share Hawayen da bayan Hannunta, Matar Ta Matukar Tausaya Mata Tace "Shiknan Kuma Bakuda kowa ne anan?" Tasneem ta gyada kai Alamar Eh, Matar Tace "Tho Zaki Iya zama dani anma kinga ni Waina nakeyi, Idan Zaki Iya zama dani tho Har zuwa Sanda Zakiga Mamanki, Sannan Inada sharadi Na farko Dole Zaki rinka min Wanke Wanke da kuma mika ma Mutane Waina" Kai Tasneem Ta gyada matar Tace "Na biyu Dole Zaki Rinka Kwanan waje wajan Kwastamomi na"...

Tho Fah Fans Shin Mai Matar take Nufi da *Kwanan Waje?* ku Biyomu Danjin Yanda zasu kwashe...

Ummu Farheen✌🏻
          N
Aysha Gana💕
[10/9, 9:55 PM] 🍹🍬🛍💍Salma🍷💍🛍🍬: [9/27, 6:03AM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
               N
*Aysha Gana*

*113 to 114*

Na Biyu Dole zaki Rinka Kwanan Waje Wajan Kwastamomina" Ina Fata Kin Ganeh?" Girgiza kai Tasneem tai Alamar Bata ganeh bah, Dan Murmushi Matar tai Batace komai bah Tahau Hada Wuta, Tasneem na gefe Har Matar Ta fara Suya Mutane Sai Layi Suke, Yan Mashin da Masu Shaguna Sunata Aikowa akai Musu, Matar ta Kalli Tasneem Tace "Tho Lokacin Aikin ki ne Yanzu dan zee bata Dawo bah", Tasneem Ta mike duk da Yunwar datake ji Nuna mata Matar Take Tana Kaiwa har Saida Cinikin Yadan Tsagaita, Tasneem Ta kalli Matar a tsorace Tace "Dan Allah Yunwa Nakeji"...

Dan Murmushi matar tai Tace "Zan baki abinci, baki fadamin Sunanki bama" Tadan Duqar dakai Sannan Tace "Tasneem" Matar Tace "Ah Suna mai Dadi" Waina Ta zuba mata Dayawa Ta mika mata, Godiya tai tasamu Guri Tazauna tasoma Ci, Wani ne lukuti Fuskarshi duk zane Yakawo Roba Ya Kalli Matar Yace "Tabawa Ya Wannan Fah?" Murmushi tai Tace "Kawo Naira Kawai Alhaji" Dan Dariya Yayi Yace "Tabawa ho bakida Kyau indai Wajan Kudi ne" Itama Dariyan Tai Tace "Kaima Kasan Kudi Abinso neh" Hannu Yasa a Aljihu ya Ciro Yan Dubu dubu Guda Biyar Ya Mika Mata Yace "Biyar ne dan Haka Kwana ne" Shewa Tabawa Tai Tace "Karka damu Karfe Takwas dai dai" Juyawa Yayi Ya kara Kallan Tasneem Yayi Murmushi Yabar Wajan...

Sai Chan Bayan Rana Tafito Wata Yarinya Wacce Zata girmi Tasneem da Kusan Shekara Biyu Ta shigo Runfar Fuskarta Dauke da murmushi, Hade Rai Tabawa Tai Tace "Dan wulakanci Sai Yanzu kika Gadaman Dawowa", Hannu Tasa a Gefen Zaninta Ta Ciro Damin Kudi ta mika mata tana Murmushi, Amsa Tabawa Tai Hannu na Rawa sai Washe Baki Take, Saida ta Kirga Sannan Yace "Allah Miki Albarka Baby Zee"...

Tabe Baki Tai takalli Tasneem Sannan tamaida dubanta ga Tabawa Tace "Wannan Kuma Fah?" Tabawa Cikeda Fara'a Tace "Yar Uwa na Samo miki, Itama duk kanwar Ja ce", Zee batace Komai Ba Tasamu Guri ta zauna, Sai bayan Azahar Suka bar wajan, Tasneem Rike da Akwatin Kayanta tana Ja, Wani Gida Suka Shiga Tun daga Zauren Gidan zaka fara jin Hayaniya, Shiga Sukai Tasneem na binsu a baya Har Bakin kofan dakinsu, Dakuna ne gidan Burjik Wanda zasukai Kusan Guda Ashirin, A bakin Kofa Tasneem Ta tsaya, Zee ta daga Labulen Sannan Tace "Shigo mana Tsayuwan me Kike?" bah Musu Tasneem ta shiga idonta cikeda Hawaye Tunawa da Naeem dinta...

Haka Naeem Ya koma Gida Zuciyarshi a jagule, a falo ya Tarar da mum Ta hade rai Tace "daga ina kake?" Yadan Kalleta Ya dukar dakai saboda hawayen dake qoqarin zubomai Yace "Daga Asibiti nake" Murmushin Takaici Mum Tai Tace "Sa'ad bai dade da barin Gidan nan ba kuma Yace daga Asibiti yake" Naeem Baice komai ba Mum Tace "Visa bazai Yuwu Yau ba Saidai gobe dan Haka jibi ka shirya barin Kasan nan" Ya dago jajayan Idonshi dake xubar da kwalla Yace "To Mum" Dakinshi ya nufa Ya Cilar da keyn dake Hannunshi Ya fada Kan Gado Yana Kuka Kamar wani Yaro, A Hankali Yake Furta why! Why mum, meyasa baki Bari nazo bah zaki Yanka hukunci, Saida Yayi Mai isarshi Sannan Ya nufi toilet...

Wanka Yayi Tareda Alwala Ya fito, Magriba da Isha Yayi Ya cigaba da Lazumi, Har Asuba Yana Tafiloli da Rokon Allah Ya baiyana mai Tasneem dinshi Yakuma Kawomai Sassauci, Saida Aka Kira Sallan Asuba Ya mike Ya Kara Yo Alwala ya Fita zuwa Masallaci...

Tasneem nazaune Tabawa Ta Fita ta miko mata bokiti Tace" Ga rijiya chan ki dibi Ruwa Kizo ga Soso idan kinci Sa'a bakowa tho Sai kije Kiyi Wankan, Tho Tasneem Tace Tareda mikewa, Bokitin ta amsa ta nufi Wajan, Sai a yanzu ta lura da Yanayin Gidan da mutanen ciki, Gida ne mai dakuna dayawa sai Daga Chan gefe data Hango Bayi Guda Biyu, Ko ba'a Fada Mata ba Tasan Daya na Toilet ne daya kuma na Wanka, Matane Burjik Kowacce na abinda Takeso daga gani Gidane namasu Zaman Kansu, Dakyar Tasneem Taja Ruwan Saboda Zurfinshi Ta dawo Tadau Kwandon Soson Ta Nufi Bayin, Allah Ya sota bakowa Dan Haka Ta Shiga, Takai Kusan Minti Ashirin Tana Tunanin Yanda zata Watsa Ruwan dan Rabonta da Wanka da Ruwan Sanyi Harta Manta...

Dakyar Tai Wankan Ta Fito, Tabawa Tabata mai Tashafa Ta Nufi Akwatinta Dan Chanza Kaya, Tana Budewa Zee Ta Matso Tace "Woaw Lallai Gaskiya Zaki zabar min Wasu kayan", Tasneem Ta Kalleta da Mamaki, Tabawa Ta mike Ta Zazaban ma Zee wayanda Zasu Mata Tace "Ai Dole Ki dauka bah Arzziki Tazo ci bah Yo ai dole a moreta itama", Tasneem Batace Komai ba sai Hawayen Dake Gangara a Fuskarta, Zee Tace "Yau zata Fara Fita neh?" Tabawa Tace "Badole ba ai Har mun Gama Magana da dan liti" Dariya Sosai Zee Tai Tareda Shewa Tace "Lallai" Itadai Tasneem jinsu Kawai Take Dan Sam Bata Fahimci komai Gameda Abinda Suke Tatauna wah bah...

Ummu Farheen✌🏻
            N
Aysha Gana💕
[10/9, 9:55 PM] 🍹🍬🛍💍Salma🍷💍🛍🍬: [9/28, 6:38AM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
               N
      *Aysha Gana*

*115 to 116*

Naeem bai Dawo Gidan bah Sai Wuraren Takwas na Safe, Koda Ya shigo Falon baiga mum bah Har Yayi Hanyar dakinshi Yaji Muryanta a Bayanshi, Ya Juyo Yadan Rusunna Ya gaida ta, Ta Amsa Bah walwala Tace "Yanzu Naeem dan na kori Yarinyan nan Shine Kaketa Kunci Ka wani daure Fuska" Kasa Amsa Mata Yayi Sai Girgiza kai da Yayi alamar Aa, Tace "Ga Kayan Break dinka Chan kan Dinning"....

A Hankali Yake Tafiya Har Kan dinning din yaja Kujera Ya zauna, Kujeran da Tasneem Tasaba Zama Ya kalla Hawaye Cike a Idonshi, Tashi Yayi ya koma Kujeran ya zauna, Duk abinda Yakeyi Mum na Kalanshi, Yanzu sam Naeem Yadaina Bata Haushi Sai Tausayi, Wata Zuciyar Tace "Ai Abinda ya dauko ne Bazai Taba Yuwuwa Bah" Ganin Baida Niyar Cin Komai Yasa Ta karasa Kan Dinning Din Ta hadamai Coffee Ta Turamai Gabanshi, Shafa Suman Kanshi Tai Ta Zauna Kujeran Dake Kusa dashi Idonta Cike da Kwalla Tace "Am Sorry Son, Eat Pls. Rabonka da Abinci fah Inaga Tun Jiya da safe" Kanshi a kasa Yajawo Cup din Coffee Ya Soma Sha, duk da Jin coffeen Yake Kamar Magani, Dakyar yasha Rabi Ya mike Yabar Wajan, Batai Yunkurin Hanashi bah saima Hawayen da suka Gangaro mata Saboda Tausayin Dan nata...

Haka Naeem Ya Yini Sukuku a daki, Duk Sanda Ya Rufe Ido Tasneem dinshi Yake Gani Tana Kiran Sunanshi, Mikewa Yayi Zumbur Ya nufi Dakinta, Yanda Yabarshi Jiya Haka Yazo Yasameshi, Teddyn daya Aje kan gado Ya dauka Ya Rungume Yana Hawaye, Murya a dishe Yake Kiran Sunanta Yana Kuka a hankali, Idonshi ne Yakai Kan Table dinda Take Zama Tana Assignment, Wani Paper Yagani Ya dauka Ya bude, Drawing ne na Mutum Sanye da kananan Kaya a Kasa Aka Rubuta *Ya Tasiu* Sai daga Gefe da aka Rubuta "i miss you", Page na Biyu Ya bude Shima Mutum ne aka zana kamar Wanchan Hannunshi Rike da Wani Zanen Kamar Mace, daga Kasa aka Rubuta *Me and my Ya Naeem* idonshi ne Yakai kan Wani dan Karamin rubutu Daya Sashi Sakin Kukan Dabe shirya bah *I Love You ya Naeem* maimaita Kalman Yake yana Cigaba da kuka...

Littafin Yadauka Ya Rungume Yana hawaye (Niko Ummu farheen Har yar Kwalla nayi, abinda ya daure min kai Shine, Shiko Naeem wanne irin so yakema Tasneem Haka?) Littafin Ya dauka ya Koma dakinshi Inda ya hada kayanshi Yasa a Ciki, Washe Gari Da sassafe Jirginsu Ya daga Zuwa "Beigin"...

     ****************

Tasneem na Zaune da Tabawa har Akai Magriba, Sam Basu nuna mata komai bah, Abinda Kawai ya daure Mata kai Shine ita idan taji an Kira Sallah Tana Tashi tayi anma bandasu, Sallama Yaro Yayi bayan sun gama chin Abinci, Tabawa Tai Murmushi Ta Amsa, Yace "Dan Litin Yace Yana Jiranki" Tabawa tace "Ganinan Zuwa" Ta Kalli Tasneem Tace "Tasneem Zo muje ki Rakani na Amso kudi" Tho Tace Ta mike Tadau Hijabinta Suka Fita, Sakin dariya Zee Tai Itama ta Fito Taja kofan dakin...

Tafiya Tasneem Taga suketayi Sunata Wuce Layika, Bata Tsinke bah Saida Taga sun Shiga wani Daki, Wani Lukutin Mutumi Tagani Zaune Yana Kallo, Ya mike daya Gansu, Tabawa Ta Kalli Tasneem tace "Tsaya a Waje ina zuwa" bah musu ta Fita tabasu Guri" Tabawa Tace "Gata saidai sabon Shiga Ce sai Kayi Hakuri" Dariya yayi Yace "Daidai Kenan" Hannu yasa a aljihu Ya kara Mata kudi Tai godiya ta Fito Tasneem Tabi Bayanta, Yace "Ina zaki Yan Mata?" Tabawa ta juyo Tace "Ki Tsaya ki amsar min Sako barin Shiga nan Gidan in Fito" Tho Kawai Tace Ta Shiga nakin tasamu Chan Gefe Ta zauna...

Yadan Kalleta Yace "Ina zuwa barinje Na amso Sakon" Tho Tace  ya fita yana dan Murmushi, Shiru Shiru bai Dawoba ga barshi Na neman Daukanta, Tun Tana jurewa Har ta sulale a Wajab ta Fara barci, Bai dawoba Sai wuraren Daya na dare, Ganin ta baje tana Barci Yasa yayi Murmushi Ya janyo Kofan Ya Karaso Inda Take Kwance...

Cikin Barci Taji ana Shafata Ta Mike a Razane ta zauna, Ganin Dan Liti Tai Yana Mata Wani Shu'umin murmushi, Ta mike Tsaye tace "Ban Sakon tun dazu shi nake kira" Ya Nufota Yace "Keh Bakya Ganewa Neh, Bah Wani sako kawai Ki Yarda dani Zaki Samu kudi Yarinya, Dukda Karancin Shekarun Tasneem Ta Gane Mai Yake Nufi, Jikinta ne Ya soma Rawa Tana Bashi Hakuri, Dariya Dan Liti Ya saki Yace "Idan Kinga kinbar nan To ki tabbata Na Cinma Burina, Bazaki sa nai Asaran Kudina bah" dam haka Zaki Yarda dani cikin Saukin kai koh ko sai nai miki da karfi, Tasneem ta zaro idanunta da sukai ja Tana Kallanshi...

Ummu Farheen✌🏻
         N
Aysha Gana💕
[10/9, 10:21 PM] 🍹🍬🛍💍Salma🍷💍🛍🍬: [9/29, 6:38AM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
               N
*Aysha Gana*

*117 to 118*

"Idan Kinga kinbar nan to ki tabbata na cinma burina, Bazaki sa nai Asaran kudina ba" dan Haka zaki yarda dani cikin saukin kai koh sai nai miki da karfi", Tasneem Ta Zaro idanunta da sukai ja tana Kallanshi...

Matsowa Ya farayi Tana Ja Baya Kuka Take Sosai Tana Girgiza Mai kai, Baya take yana biyota bata ankara bah ta fada kan Katifar shi, Murmushi Yayi Yace "Daidai knan Yan mata", Biyota Yayi kan Katifan Ta fara Rarrafe Tana Kokarin Sauka anma ina!, Kamota Yayi Ta Saki Kuka dakarfi Tana Bashi Hakuri, Hijab din Jikinta Ya cire Yayar, Kwantar da ita Yayi Tana kuka tana zuzulewa kokarin Ciremata Riga Yakeyi, Juyawan da zatai Ta hango Kwalban 7up kusada ita, Tureshi Tai da karfi Yayi baya kamar zai Fadi Hakan ya bata daman daukan Kwalban...

Mikewa Tsaye Tai, Ya Matso Ta Kalleshi Cikin Kuka tace "Ka rabu dani, idan ka matso sai na kwala ma" Dariya yayi Yace "Lallai Kin Cika jaruma duk da banga jarumtar taki bah" Ganin Yana Kokarin Matsowa Yasa Ta kara Gyara tsayuwa ta rike Kwalban Dakyau, Kokarin Rikota Yake Ta rintse ido da karfi ta buga mai Kwalban Har saida Ya fashe...

Bude ido tai a hankali taga Yana Kallanta, Kwalban Ya fashe mai akai, Ganin Yanda Jini ke fita Yasa Ta kwalla Kara da karfi, Zubewa dan Liti Yayi a wajan, Tasneem na ganin Haka Ta kara Sakin ihu Ta yi hanyar kofa, Tako ci sa'a bai rufe bah, dagudu tafita daga dakin, Gudu kawai Take batareda Tasan inda zata bah, Kuka take bah kakautawa Tanayi Tana Cigaba da gudun, Saida Taji ta gaji Sosai Sannan Tasamu gefen wani Gida Ta zauna, Naeem ne Ya fado mata a rai, Ta kara sakin Sabon Kuka tana kiran sunanshi a hankali, A haka Ta sulale barci mai Nauyi Ya dauketa...

       *************

Da Sassafe Mum Ta Shiryo Ta janyo Trolleynta takai Bakin mota, Shiru bataga Naeem ba Yasa ta shiga dakin da Sallama, kwance tasameshi Cikin bargo sai Rawar sanyi yake, Idanunshi a rufe hakoranshi Sai karo suke da juna, A Razane ta karasa Gaban Gadon Ta Taba Jikinshi Taji Zafi Rau sosai, Idonta Suka Ciko da kwalla Ta Kalli Agogo taga Saura Awa Biyu Jirginsu Ya Tashi, Kallanshi Tai Cikeda Damuwa Tace "Sorry son but we have to live" Ganin Bakinshi na Motsi Yasa Takai Kunenta Daidai Saitin Bakinshi, Abinda Taji Yacene Yasa ta Hade Rai Ta mike Tabar Dakin, Tasneem! Tasneem!! Yake Fada dakyar Idanunshi a rufe...

Layin Sa'ad Ta soma nema, Bai Dade da fara Ringing ba yadauka, Cikeda Ladabi ya gaidata ta Amsa, Tace "Dan Allah Sa'ad Karka Gaji dani i still need your Help" Sa'ad Yace Lapia?" Mum Muryanta na Rawa Tace "Wallahi Son neh" Sa'ad Najin Haka Ya Katse wayan, Cikin Mintunan Da zasu kai Talatin ya iso Gidan, Direct Dakin Naeem Ya Shiga mum Tabi bayanshi, Yanda Ta barshi haka Sukazo Suka sameshi, har Yanzu bai daina kiran Sunan Tasneem bah...

Tayar Dashi zaune Sa'ad Yayi Yace "Be Strong Naeem Pls" BP machine Ya dauko ya gwadashi, Yayi Matukar Razana da ganin Reading din, Ya dauko Thermometer Shima Ya Gwada shi, Mum Dake Gefe Tace "Pls Sa'ad Try your best Just Give Him First Aid Muna Zuwa Chan Sai muje a Dubashi Sosai", Sa'ad Ya Kalli Mum Yace "Ina zaku mum?" Tace Zamu koma Beigin Alhaji Yace Mu koma, Sa'ad Baice komai bah, Magani Ya babala Ya Kalli Mum Yace "Yakoci wani abu?"..

Kai Ta girgiza Yace "A samo mai ko tea ne Zai Sha Magani, A gurguje Ta hado ta kawo, Dakyar Sa'ad Ya Samu Yabashi Yasha Kadan Sannan Yasha maganin, Shima Saida akai fada, Sa'ad dakanshi ya Hada Mai Ruwa a Toilet Ya Taimaka mai Ya shiga, Kallan Mum Yayi Yace "Mum Pls Kiyi Hakuri, Naeem na Matukar San Tasneem Ni shaida ne mum, Kinga Yanzu Yanda Bp Dinshi Ya tashi I was very suprise" Mum Batace Komai Bah Hankalinta a tashe...

Naeem Ya dade Sannan Ya fito mum ta kalli Agogo Taga Saura 30mints Jirginsu Ya daga, Dakanta ta fita da Akwatin Kayan Naeem Tasa Driver Yasa a Mota, Bashi Baki Sa'ad yake har Ya samu Ya shirya, Rikoshi Yayi Har bakin Mota Ya Shiga, Sa'ad Ya musu Fatan Alheri, Shidai Naeem ba Umm Bah u'umm har Driver Yaja Motan Suka bar Gidan, Suna isa ana Kira, Dan haka Ba'a dau lokaci bah Aka Gama Komai mum ta rikoshi Suka Shiga jirgin, Bayan kowa Ya shiga Kofa ta rufe Jirgi Ya daga...

                **
Sanye Yake da Yar Farar Jalabiya Sauri Yake dan ya makara har an Soma Raka'ar Farko, Hannunshi Rike da Torch Light Dan Yasan Sauran Anguwan bah Wuta, Dakin Mai Gadi Yayi Magana Yace "An Tayar fah" Mutumin Dake Dakin Yace "Tho Yallabai" Kofar Gidan Ya bude Ya fito, Kanshi a Sama Yana Sauri kar a Tsere mai raka'an Farko Yaji Yayi Tuntube Da Abu, Saura kadan Ya fadi, Haskawa Yayi Daga Mutum Shame Shame a kwance, Dasauri Ya dawo Baya, Haskawa Yake Sosai Har Yakai kan Fuskanta, Fuskan da Yagani ne Yasa Ya Zaro ido Tareda Zakin Torch Light din...

Shin Fans Wanene Wannan?? Nidai Nace....🤔"Ku biyomu dan Jin Wanene Wannan har dasu sakin Torch Light..


Ummu farheen✌🏻
            N
Aysha Gana💕
[10/9, 10:21 PM] 🍹🍬🛍💍Salma🍷💍🛍🍬: [9/29, 5:16PM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
               N
*Aysha Gana*

*119 to 120*

Haskawa Yayi Yaga Mutum Shame Shame a kwance, Dasauri ya dawo baya, Haskawa Yake Sosai Har Yakai kan Fuskarta, Fuskan da Yagani ne Yasa Ya Zaro ido Tareda Sakin Torch Light dinda ke Hannunshi, Kura Mata Ido yayi Yaga Ta Gyara Kwanciya Ta Cigaba Da barcinta, Daukan Torch Light din Yayi Ya kashe Yasa a Aljihu, matsowa Yayi Kusada Ita Ya Rasa Ta ina zai Fara, Yakai Musan Minti Uku a Tsaye Chan Ya dake Ya Dauketa Chak Kamar Wata Baby Ya sabata a Wuya Ya Shiga da ita Ciki, Yaci Aa Mai Gadi bai Fitowa dan haka Side dinshi Ya wuce da Ita, Kan gado Ya kwantar da ita Ya Rufeta da bargo...

Har Yayi Hanyar Fita Yaji an Sallame Sallah, Oh! Yace Ya Shimfida Sallaya Ya tayar da Sallah, Saida Ya idar Yayi azkar tareda Karatun Alkurani, Sannan yadawo Bakin Gadon Yadan Tsuguna, Kallanta Yayi Sosai Tabbas itace, Tho meya kawota bakin Kofar nan?? Sake Sake Yaketayi Har Gari Yayi Haske, Wanka Ya shiga Yayi Ya Fito Ya Shirya Cikin Riga Polo Fari Gabanshi an Rubuta "Jagaban" Sai Wando Jeans, Suman Kanshi daya sha Wanki ya shafe Da mayuka Masu Kamshi dakuma Sa Gashi Santsi da Kyalli, Juyawa Yayi Ya kalleta Yadanyi Murmushi Sannan Ya fita...

Tasneem bata Farka bah Sai Wuraren Karfe Goma, A hankalu Take bude ido Tareda Mika, Ganin Inda take Yasa Ta mike Zaune Dasauri Tana Kalle Kalle, Ganin Dakin Tai Kamar na Ya Naeem, Murmushi Ta saki ta diro daga Kan Gadon Dasauri, Bude Dakin Tai a hankali Ta fito, Falo ta gani dan Madaidaici, Ganin ba Gidan Ya Naeem baneh Yasa Ta Saki kuka, Hanyan Kofan Ta nufa Ta murda, Jitai a Rufe Tasake sakin Kuka da Karfi, Lungu Lungu ta Shiga Lekawa Bataga Kowa bah, Falon Ta dawo ta zauna bakin Kofan Ta Hada Kai da Guiwa ta Cigaba da Kuka, Kuka Take sosai ba kakautawa a Wajan, Bai Dawoba Sai wuraren Shabiyu Saura, Key Yasa ya bude Kofan, Tanaji an Bude kofan Ta dago kai dasauri, Ganinshi yasa ta Mike Dasauri, A Hankali Ta furta *Bature!* Qura Mata Ido Yayi, Ja baya Ta soma Yayi Yadanyi Murmushi Yace "Bah Abinda Zan miki"...

Zaro ido Tai Ta Bude baki, kasa Haquri Tai tace "Lah Kanajin Hausa" Murmushi Yayi Dimple Dinshi Suka Lotsa, Ta Kara Bude Baki Tace "Lah Irin Abuna" Yadan Kalleta Yace "Mene" Dimble Dinta ta taba, Yadanyi Dariya Mara Sauti Yace "Me Kikeyi a Waje Jiya?" I Mean Meya Faru naganki da asuba a Waje?" Idonta Ya ciko da Kwalla, lokaci kadan Ta fara Kuka Tana Yarfe Hannu, Ohh! Yace Y are You Crying, Pls Kidaina Fadamin kinji Sis" Labarin Abinda yafaru itada Dan liti ta bashi, Mamaki ne fal a Fuskanshi Yace "Tho Mai Ya Kaiki Wajan Matan Har Takaiki Wajanshi??"...

Wuri Tasneem Tasamu Ta zauna Tana matsar Kwalla, Labarin Ta Tun Sanda take Wajan mallan har Lokacinda Ta Gudu Daga Dakin Dan liti Ta bashi, Dagowa Tayi taga Yana share Hawaye, Tace "Meyasa Kake kuka?" Girgiza kai Yayi Sannan yace "Bakomai" Murmushi kawai tai ta Sadda kai kasa tana Wasa da zoben da Naeem ya bata Ranan Birthdayn tah, Yace "Menene Sunanki?" A Hankali tace Tasneem" Murmushi Yayi Yace "Nice Name" Ya Kalleta yace "Kinajin Yunwa Koh?" Kai Ta gyada mai, Ya mike Yace "Ina zuwa" har Yakai Bakin Kofa ya juyo Yace "Bakimin Gwallo Bah" Dariya Tai Ta Dukar dakai, Shima Dariyan yadanyi Ya Fita...

Main Building din Gidan ya nufa, Falon Ya shiga da Sallama, Bah Kowa a Falon Ya Haura sama Zuwa Dakin Mami, Knocking Yayi a Kofar Yace "Mamina Were are you Kin barni inata Doka Sallama" Daga Cikin Dakin tace "Come in" Ya shiga Yana Bata Fuska Cikeda Shagwaba Yace "Mami Am Hungry" Zaro ido Tai Tace "Ya salam! Na manta Ga Break dinka chan a Kasa, I tot Nace Sa'a Takai maka" Girgiza kai Yayi cikeda Shagwaba, Ta mike Tace "Muje Kaci To, Am Sorry Ta shafa Suman kanshi Tana murmushi"...

Hannunta Ya Rike Ya zaunar da ita yace "Wait Mum I hav Something to Tell You" Ta Kara shafa kanshi Tace "Ok Am all ears Sweetheart", Murmushi Yayi Saboda sunanda Ta kirashi Yana Son Sunan, Ya Gyara Zama Cikeda Murmushi Yace "Mami i Finally Got Her", Cikeda rashin Fahimta Mami Tace "Wah?" Shagwabe Fuska Yayi ya turo Baki Kamar karamin yaro Yace "Ohhh! Mami, Wacce Nace Miki Ina Ganinta idan Na Fita," Mami I Told Uh I love Her, She's Cute Ohh!"...(Niko nace Wallahi baka isa bah, Naeem Zamuba, #Murguda baki#)

Dan Dariya Mami Tai Tace "Nah tuna Swtheart, Tho aina Take? Who is her Fader?" Ya Girgiza kai yace "Bah Yarinyan Kowa bneh" Infact She Dnt Knw Her Parents!" Mikewa Tsaye Mami Tai tace "What are you Talking About?" Mikewa Yayi ya zaunar da ita bakin Gadon Ya Tsugunna Wurin Kafanta, Labarin Tsintanta Yaba Mami Da kuma labarin da tabashi", Hawaye ne Shabe shabe a Fuskan Mami, Tace "Na Tausaya Mata But are You Sure she's Telling the Thruth?" Kai Ya Gyada Tai Shiru Tareda Goge Hawayen dake Fuskanta tace "Were is she now?" Yace "Tana Side dina" Mikewa Tai Tace "Muje in Ganta"...

Yana Tafe Tana Binshi a baya har Suka sauko, Sa'a Ta Kwallawa Kira Tace "Ki Kawo ma Son Abinci Side Dinshi" Daga Cikin Kicin Ta amsa da Tho, Side Din Suka Shiga Inda Ya Barta nan Yazo Ya sameta, Tanajin Sun shigo ta dago Suka Hada ido da Mami, Dam! gaban Mami ya fadi...

Tho pha...Mudaije Zuwa!

Ummu Farheen✌🏻
            N
Aysha Gana💕
[10/9, 10:21 PM] 🍹🍬🛍💍Salma🍷💍🛍🍬: [10/1, 8:00PM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
               N
*Aysha Gana*

*121 to 122*

Yana tafe tana binshi a baya har suka sauko, Sa'a ta kwallawa kira Tace "ki kawoma son Abinci side dinshi" Daga Kitchen ta amsa da Tho, Side Din Duka Shiga Inda Ya Barta nan Yazo ya Sameta, Tanajin Sun Shigo ta dago suka hada ido da Mami, Dam! Gaban Mami Ya fadi...

Kurrri Mami Tai Mata Tana Kallanta, Yace "Mami Itace", Dan Murmushi Mami Tai ta karasa Kusada Tasneem Tace "Yes She's Cute" Ta sa Hannu Ta dago Haban Tasneem Tace "Menene Sunanki?" A Sanyaye Tace "Tasneem" Kin Tabbatar da Labarin da Kika bah Faizan? Gyada Kai Tasneem Tai, Mami Tace "Shiknan", Ta Kalli Faizan Tace "Sai Mun Jira mai Abbanka zaice idan Yadawo", Kan yayi Magana Sa'a Tai Sallama Hannunta Dauke da Tray, Suka Amsa Ta aje Ta fita, Mum Tace "Bata Abinci Taci, Idan Tagama Tadawo Chan Side din Zuwa Sanda Abbanka zai dawo muji Hukuncin da zai Yanke", Tho Faizan Yace Mami Tabar Side Din Cikeda Tunanin Tasneem, Lallai Tana Mata Matukar Kama da Wani koh Wata Anma Sam Ta manta inda Tasan Fuskan..

Lokaci Guda Taji San Tasneem ya Shigeta, Cikeda Murmushi ta koma Side dinsu..

Tasneem Ta kalleshi Tace "Mainene Sunanka?" Yadanyi Murmushi Yace "Bakiji Mami ta kira Sunana bah??, Ta girgiza kai Alamar Aa Yace "Sunana Faizan" Tace "Umm Sunan Yan Gayu Ban Tabajin Sunanba" Murmushi Kawai Yayi Ya Xuba Mata Abincin Ya mika Mata, Kurrri Tamai Tana kallanshi Yace "Eat mana Sis ko kinaso nabaki a baki??" Kai Ta girgiza Alamar Aa...

Fork din ta dauka Ta Fara Ci, Idonshi ne Yakai kan Zoben Dake Hannunta, Ya kalleta Yace "Waya baki Wannan Zoben?" Ta Kalli zoben Ta maida Dubanta ga Faizan Idonta cikeda Kwalla tace "Ya Naeem ne Yabani" Murtuke Fuska Yayi Yace "Pls ki Cire Kinga Fah Yanzu bakwa Tare" Girgiza Kai Tai Tana Kallanshi Tace "I promise him bazan Taba Cirewa bah" Baice mata Komai bah Har ta gama, Ya Kalleta Fuska bah Walwala Yace "Muje Wajan Mami"...

Bah Musu ta mike Tabi Bayanshi Har Side din Mami, Suna Shiga Tasneem Ta Saki baki Sai Kallan Gidan Take, Tunda Take bata Taba Ganin Gida mai Kyau Irin Wannan Bah, Duk da Cewa Gidan Naeem ba Baya Yake bah, Amsa Wannan yafishi Kyau da Komai..

Gani Tai Ya haura Sama Ta Bishi Dasauri, Dakinda Ya tura ya shiga da Sallama Itama Ta shiga, Zaune Suka Sami Mami Kan Gado Tana waya, Saida Ta gama Sannan Faizan Yace "Gata" Murmushi Mami Taima Tasneem Tace "Dawo kusa dani kinji" Mikewa Tasneem Tai Tadawo Kusada Mami Ta zauna, Mami Tadan Rungumota Tace "Zaki Zauna Damu?" Kai Tasneem Ta gyada Sannan Tace "Anma Ku fara kaini Wajan Ya naeem da Mama Laraba" Shiru Mami Tai, Faizan ya mike tareda Hade Rai Yace "Idan Muka Fita zaki Ganeh Gidan??" kai Tasneem Ta Gyada Yace "Tashi Muje Tho"...

Mikewa Tasneem Tai Mami Tai Saurin Riketa Tace "Tsaya To mana kiyi wanka, Dakyar Ta Shawo Kan Tasneem Tai Wanka, Driver Tasa Ya Kai Sa'a kasuwa aka Sayo mata Kaya Masu kyau da Tsada, Daya Ta zabar Mata Tasa Sannan Suka Tafi, Yawo sukai Sosai har yanma Tasneem bata Gane Gidan bah, Haka Suka karaci yawon su duk sun gaji suka dawo gida..

'Mami Tace "Nidama Nasan Bazata Ganeh Gidan nan bah, Faizan Ya kalli Tasneem Yana dan murmushi Yace "Duk in bamu Wahala" Mami tace "Sorry!" Baice komai bah Ya mike Yace "Pls Mami am Hungry ina Side dina" Bai Jira mai Zatace bah Ya Bar Falon!, Sa'a Ta kwalla wa Kira, Abincin Ta hado a Tray Ta Nufi Kofan Falon Zata Fita, Tasneem dake gefen Mami Tanacin Nata Tace "Mami in Bita?" Aa keda kikecin Abinci ki bari ki Gama, Zumburo Baki Tasneem Tai Ta Cigaba da Cin Abincin, Dan murmushi mami Tai, Itadai Allah ya Daura Mata san yaya mata Gashi Allah bai Bata bah, Kallan Yanda Tasneem Take Cin Abinci Take Cikeda shawa'a...

Tana Gamawa Ta muke dagudu Tabar Falon, Side din Faizan Ta nufa, Murdan Kofan Tai ta Tura a hankali, Zaune ta sameshi kan Two Seater Ya aje laptop akan Cinyanshi Yana buga Zuma, Dagowa Yayi Ya kalleta Yasakar Mata Murmushi, Karasawa Tai Ta zauna kusada shi Tana Kallan Yanda Yake Bugawa, Saida Ya buga kusan Stage Biyar sannan Yasa Pulse Ya janyo trayn Abincin...

Tasneem Ta dauka Tana Kokarin Dannawa Yace "Meh Zakiyi?" Turo Baki tai Cikeda Shagwaba Tace "Nima Zan buga ne" Yadanyi Murmushi Yace "Tho kin Iya neh?" Girgiza kai Tai Alamar Aa Sannan Tace "Anma ai naga Yanda kakeyi" Baice Mata komai ba Ya Fara Cin Abincin shi, Tana Ganin Haka Ta Janyo Laptop din ta soma Shige Shige!, Game din Taga Ya bace, Shige Shige Take tayi Ta goge Wanchan Ta Goge Wanchan, Ganin Barnan Datamai Yasa a Aje System din Sadaf Sadaf Tabar Falon, Kiran Sunanta Yake Tanaji Ta Arce a dari da sittin....

Zakumin Afuwa na Rashin Posting Ina Karatu ne Ranan Talata Xan Fara jarabawa, Ina baran Adduar ku Fans..Thanks

Ummu Farheen✌🏻
            N
Aysha Gana💕
[10/9, 10:21 PM] 🍹🍬🛍💍Salma🍷💍🛍🍬: [10/4, 6:00AM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
            N
     *Aysha Gana*

*123 to 124*

Tana Ganin Haka Ta janyo laptop din ta soma shige shige, Game din taga ya bace, Shige shige take tayi ta goge Wanchan ta goge wanchan, Ganin barnan datamai yasa ta Aje systen din sadaf sadaf tabar Falon, Kiran Sunanta Yake Tanaji ta arce a dari da Sittin...

```Naeem Fah?```

Zazzabi ne Sosai Ya rufe shi a Cikin Jirgi, Bah Karamin Tashi Hankalin Mum Yayi Bah, Rungumoshi Tai Ta daura kanshi akan Kafanta, A hankali Take Shafa mai baya Har Barci Ya daukeshi Dakyar, Dukda duk Wanda Yaga Barcin Yasan Bana dadin Rai baneh....

Karfe Bakwai na dare Jirginsu Ya sauka, Ma'aikatan Jirgin Sukai Waya aka taho da Ambulance, Suna Saukowa Mum Ta hade da dad Yana Jiransu, Ganin Naeem Kwance akan Gadon Ambulance Yasa Ya zare ido Yace "What Happen to my son" Shiru Mum Tai kanta a kasa Tana Hawaye, Baice komai Ba Tasa Kayansu a Booth din Motan Ta Shiga Yaja Suka Fara bin Motan Asibitin...

Tafiya suke lokaci lokaci Yakan Furxar da iska Tareda Dukan Stearyn Motan da Hannunshi na Dama, Saida Suka iso Asibitin Yanayin Paking Ya Juya ya kalleta Yace "If any Thing Happen ti my Only son...Gwafa Yayi Ya fita tareda Banko Kofan Ya Shiga Cikin Asibitin, Mum Mutuwar Zaune tai Hawaye Kawai ke Gangara daga Idonta, A Hankali Take Furka "Am Sorry Son!, Am Sooo Sorry" Fashewa Da kuka Tai Tana Tuna Irin Korar Dataima Tasneem da Mama Laraba...

Saida Tai Kukan Mai Isanta Sannan Ta mike Ta shiga Asibitin, Tana Shiga Litikan na fitowa daga Dakin, Dan Tsayawa Tai Duka Wuce Sannan Ta Murda Kofan Dakin a hankali Ta Shiga, Kwance Ta Sameshi Ana Samai Drip, Sai Gefenshi Magunguna da aka Cicire guda Daya, Alamar an Bashi, Idonta ya ciko da Kwalla Ta Karasa Bakin Gadon Ta zauna, Hannun Tasa Ta shafa Suman Kanshi Tadanyi Murmushi Hawayen Dake Makalle a idonta Suka gangario Tace "Am Sorry Son, Nama Alkawari sai Tasneem Ta dawo gareka I promise you"...

Gyaran Muryan dataji a bayanta ne Yasa Tadan Juya A hankali, Wata Likita ce Ta Shigo Da Sallama, Sanye da Dogon Riga Abaya Sai Lap code dake Saman Rigan, Fara ce Sosai, Saika Kalleta Sosai Zaka ganeh Yar Nigeria ce, Mum ta Kalla Tace "Sannu Mah" Gyada Kai kawai Mum Tai, Ta kara Murmushi Tace "Ya Jikin Naeem din?" Mum ta Kalleta da mamakin Hausan datai Tace "Dasauki" murya a Sanyaye, "Allah kara Sauki" Tace "Ta murda kofan Dakin Ta fita Tana Mai Jin Dadi, Lallausan Murmushi Ta saki Ta koma Office Dinta Tanata jin Dadi...

_Fans Ita kuma Wannan Fah??_( mudaije zuwa)

Bayan Isha Tasneem Nazaune itada Sa'a a falo ta kunna mata Mbc3, Takurewa Tasneem Tai a gefe hankalinta Sam Baya Wurin Kallon, Faizan ne Ya shigo Falon da Sallama, Sa'a Ta amsa tareda Mikewa Tabar Wajan, Ganin Halin da Take ciki Yasa Ya karasa Ya zauna kusada ita Yace "Sis Whats Wrong Meke Damunki??" Girgiza kai Tai alamar bah Komai, Gyara Kwanciyar datai Kan Kujeran Tai, Anan Yaga Hawayen Dake Kwance Kan Fuskanta, Gabanshi ne ya fadi Yace "Pls Sis Kidaina Kuka kinji"...

Handkie Yasa Ya Goge Mata Hawayen dake Fuskanta Yace "Tell me Why are You Crying??" Kallanshi Tai ta kara fashewa da kuka tace "Ya Naeem" Wani kololon Abu yaji a Kirjinshi da makoshin Shi Ya danne Yace "Tho yanzu ai Baya nan ki daina kuka kinji?" Duk Abinda Yake Miki Nima Zan Miki" Kara Goge Hawayen Dake Fuskanta Yayi yace "Bulala nazo namiki fah" Ta zaro ido Cikeda Shagwaba tace "Menayi" Dan Murmushi Yana San Shagwabar Ta, Ya kwaikwayi Yanda Tai magana Yace "Koba ke Bace dazu Kika Goge Mun Abubuwana Na System" Ya kare Maganan Yana Turo baki Tareda Rungume Hannu, Kyalkyalewa Da dariya Tai Tace "Kamar Ya Naeem" Dan gintse Fuska Yayi Ya Sasauta Murya Yace "Ki daina Fadin Ya Naeem Kinji Am now Your Brother"...

Kai kawai Ta gyada a Kalleta Murya a Sanyaye Yace "I Love You Tasneem, I love You soo Much" Dagowa tai dasauri Ta kalleshi, Duk da Bayau Ta Saba Jin Kalman Bah, Anma Nayau sai Ya mata nauyi, Muryan Mum Sukaji Tana Cewa "Ku tashi Kuban Guri inyi Kallo, Su o'I An Girma ba'a San an Girma bah" Turo Baki yayi ya mike Yace "Nidai Mami Bakya Sona yanzu bakomai" Yanzu Ko irin Babyn nan ma kin daina kirana, Dariya tai Tace "Kai Yanzu Kazama Kato Ka Girma" Ta Rungumo Tasneem Tace "She's Now My Baby"..

Dariya Tasneem tai Ganin Yanda yake Bubbuga kafa a kasa yana Turo baki, Mami Tace "Ahan kan Na manta Tomorrow by 9pm Abbanka fight dinsu Zai sauka Zamuje mu taroshi, And kai nakeso Kai Driving Muje" Ihu Ya saki Kamar Karamin Yaro Yace "Nima Wanda yake Sona Zai Dawo" Yabar Falon Yana dariya tareda Dagama Tasneem Hannu..

Tasneem Ta kalli mami Tace "Mami nima Zan Raka ku" Mami Tace "Aa Tasneem Ki Bari Idan Mukaje Muka dawo i promise you zan Kaiki Yawo" Girgiza Kai tai Tana Turo baki, Mami Tace "Oh Allah! Tasneem Rigima, Faizan Rigima" tace "Shiknan naji zamuje Tare" Rungume Mami Tai Tana Murmushi...

Ummu Farheen✌🏻
            N
Aysha Gana💕
[10/9, 10:21 PM] 🍹🍬🛍💍Salma🍷💍🛍🍬: [10/4, 9:11PM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
                 N
       *Aysha Gana*

*125 to 126*

Tasneem ta Kalli Mami Tace "Mami nima Zan Raka ku" Mami Tace "Aa Tasneem ki Bari Idan Mukaje Muka Dawo i promise you zan Kaiki Yawo" Girgixa kai tai Tana Turo Baki, Mami Tace  "Oh Allah! Tasneem Rigima, Faizan Rigima" Shiknan naji zamuje Tare" Rungume Mami Tai Tana Murmushi...

Kwallawa Sa'a Kira Tai Ta Amsa Ta Taho dasauri, Mami Tace "Kaita Dakin Dake Kusada nawa I hope a gyare Yake??" Eh Tace Ta mike, Mami Ta kalli Tasneem dake Manne a jikinta kamar sun dade da sabawa Tace "Dare Yayi go and Sleep gobe sai Kixo kiban Labari irin Wanda kikaba Faizan" Gyada kai Tasneem tai Ta mike Ta Hau Sawa Tana Bin Sa'a, Har sunyi nisa ta dawo dagudu Tace "Good Night Mami" Juyowa Mami Tai Da Murmushi dauke a Fuskanta tace "Good night My Baeby" Dagudu Tasneem Ta koma Ta Shiga Dakin, Komai Dangane na Bukata akwai a dakin, Tunawa da yanda Dakinta Yake a Gidan Naeem Yasa Ta bata Rai Ta Turo Baki, Side Lamp din Takashe Ta haye Lallausan Gadon taja Blanket..( _Anan Zance Good Night Tasneem din....?lol_)

Da Sassafe Mami Ta Fita Bayan Tama Sa'a Bayanin Abinda Zata Dafama Faizan da Tasneem, Tasneem Bata Farka bah Sai Karfe Tara, Ahankali ta juya Tareda Karanto Adduan Tashi daga Barci, Mikewa Zaune tai Tareda Hamma, Cikin Magagin Barci Ta sauka daga Kan Gadon Tareda Mitsitsike ido da bayan Hannu..

Toilet ta Shiga Tai Alwala Ta Fito, Ganin bah Kaya a dakin Yasa Ta fito, Dakin Dake kusada Nata Ta Murda Ta Shiga tana Zazzare Ido, Murmushi Tai Tace "Dakin da mukaxo Jiya" Walldrop din Dakin Tahau Bincikewa Har Ta samu Hijab, Dakinta ta koma tasa Tai Sallan Ta Aje Akan Gado Ta fita, Saukowa Daga Steps din Take a hankali Tana Lekan Kasan, Bah Kowa a Falon, Ta karasa saukowa Ta Nufi Kofar Falon, Muryan Sa'a Taji Tana cewa Ga Breakfast Dinki a Dinning Kizo Kici...

`Turo Baki tai batare da Ta juya ba tace "Sai Mami Ta tashi Sannan Zamuci Tare", Sa'a Dake Bayanta Tace "Ai Mami ta fita Tun Dazu" Tasneem Ta juyo Tace "Dagaske??" Gyada kai Sa'a Tai, Shiru Tai tana Tunani Lallai bata nan Tunda Dazu Ta shiga dakin Ta bincike Mata Kaya kuma bata ganta bah, Batace komai ba Ta fita haraban Gidan...

`Dai dai nan Faizan Na Shigowa Sanye da Riga Da Dogon Wande Irin na sport, Kafarshi Sanye Da Faran Hadadden Canvers Daga gani Daga Morning Excercise Yake, Yana Kokarin Shiga side Dinshi baima Hangota bah, Tace "Ya Faizan Were are You From?" Ya Kalleta da mamaki Yace "Har Kin Tashi??" Infact Waya Koya miki Turanci Becose You Told me Daga Kauye Kike" Sakin baki Tai tana kallanshi, Yayi Murmushi Yasa Hannu ya rufe Mata bakin Yace "Tho madam Rufe Bakin Kafin Miyon Ya fara zuba", Rike Kugu Tai Tace "Koba kai bane a motanka Kakemin Gwallo idan za'a Kaini School"...

Sosa keya Yayi Yace "Oh Yes You Right" Ooh Ni Nake ma Miki gwallo koh?" batace mai Komai ba ta juya Tana Kokarin Komawa Falo, Yace "Anjima Zamu Fita idan Mami Tadawo Tel her" Juyowa Tai Tace "Dagaske??" Gyada Mata Kai Yayi Yana Murmushi, Dagudu Ta Shiga Falon, Kan Dinning Ta zauna Tahau Cin Abincin...

Mami Bata Dawo Gidan Bah sai Bayan La'asar, Tasneem Nazaune Tana Kallo Itada Sa'a Sukaji Shigowan Motan Ta, Dagudu Tasneem Taje Ta rungumeta Tana Mata Sannu da Zuwa, Mami Ta Kalli Tasmeem Tai Murmushi Tace "I Hope Bawani Matsala koh?"...

Turo Baki Tasneem Tai Tace "Akwai", Mami tace "Tho mushiga Daga Ciki Muyi maganan", Direct Dakinta Ta Shiga, Waldrop dinta Tagani a bude Wasu kayan duk a Kasa, Sa'a Ta kwallawa kira Tace "Garin Yaya Haka?" Kan tai Magana Tasneem Tace "Dazu ne dazan dauki Hijab nai Sallah" Murmushi Kawai Mami Tai Tace "Am Tired Yau Gobe Sai Muje Nasai Miki kaya koh?" Gyada Kai Tasneem Tai Cikeda murna...

Shirye Shirye Ake Sosai Dan Yau Alhaji zai Dawo daga dubai, Mami da sa'a bah Zama sai Shige Da Fuce Suke, Cikin Lokacin Kadan Gidan Ya kaure da kamshi, Tasneem Ko Duk Inda sukai tana biye Dasu Tana Chokallo Musu Tambaya ( _ina Fata baku manta da tasneem ba fagen Tambaya_) Faizan Bai dawo Gidan bah sai Karfe Takwas Lokacin Har Tasneem Tai Barci...

A Gurguje Suka Tafi Airport din, Karfe Tara Dai dai Jirginsu Ya sauka, Abba na saukowa Faizan ya tafi dagudu ya Rungumeshi, Murna Sosai Abba yayi da Ganin dan Nashi Kwaya Daya tal, Duk Suka Dungumo Suka Dawo Gida, A tare Sukai Dinner Cikeda jin Dadi Da Anashuwa, Duk Wainar da ake Toyawa Tasneem Nachan Tana Sharban Barci...

Washe Gari da Safe, Hayaniyan Da Tasneem keji a kasa Yasa Ta farka, A Hankali ta Diro daga kan Gadon, Fitowa tai Taji Muryan Faizan a Kasa Wajan Dinning, Da gudu Ta sauka daga stirs din Ta nufi Dinning din, Dai Dai Nan Abba Ya Dago Suka Hada Ido Da Tasneem Ya Mike Dasauri Yana nunata muryanshi na Rawa...

Ummu Farheen✌🏻
          N
Aysha Gana💕
[10/10, 3:46 AM] 🍹🍬🛍💍Salma🍷💍🛍🍬: [10/5, 6:51PM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
               N
        *Aysha Gana*

*127 to 128*

*Tsokaci kadan Dangane da post dinda aketa yayatawa nacewa Ummu Farheen Tayi, Ni Ummu Farheen Bansan da Post din nan bah, Menene Ribana Idan na Zagi Writers Yan Uwana?? Haba Yan Uwa yakamata Kumin Uzuri. Idan kunga Abu Yakamata Kafin Ku dau mataki ku Fara Bincika wah...Wannan Post din da aketa Yayatawa Nafada na sake Fada bani nayi bah..Sannan "Gareki koh Gareka Wannda Kika ko Kai Posting din Nan Bah Abinda Zance Sai Allah Ya isa, Kuma Sai Allah Yabimin Haqqi na Akan Abinda Kika ko Kai Min...Nagode Writers Yan uwana da Kuka Fahimceni, Allah Ya barmu Tare Gaba Daya Ameen..*

Washe Gari da Safe, Hayaniyan Da Tasneem Keji a kasa Yasa Ta farka, A Hankali ta Diro daga kan Gadon, Fitowa Tai Taji Muryan Faizan a Kasa Wajan Dinning, Da gudu Ta sauka daga stirs din Ta nufi Dinning Din, Dai dai nan Abba Ya dago Suka Hada Ido da Tasneem Yamike Dasauri Yana Nunata Muryanshi na Rawa Yace "Taaasneem!"..

Karasowa Tai Tana Kallanshi Tace "Alhaji me kazoyi Nan gidan??" Mami ce Ta mike Tace "Alhaji Kasanta neh??" Ya Gyada kai Yace "Kwarai kuwa Itace Yarinyan dana Baki Labari" Mami Ta juya ta kalli Tasneem Da Mamaki, Faizan Koh Mutuwan zaune Yayi Yana Kallansu Daya Bayan Daya, Mami Ta Karasa Kusada Tasneem ta kamo Hannunta Ta zaunar da ita...

Zama Alhaji Yayi Cikeda Mamaki, Kan Yayi Magana Tasneem Tace "Alhaji Mekazo yi nan Kasansu neh?? Inata Nemanka Ban Ganka bah, Idonta Ya ciko Da Kwalla Tace "iya ce Tace Zatamin Aure Shine na gudo" Alhaji Yadan Mata Murmushi Ya Juya Ya Kalli Mami Alamar neman Karin Bayani", Gyaran Murya Mami Tai Taba Alhaji Labari Kamar Yanda Faizan Ya Fada Mata, Alhaji Cikeda Tausayawa Yace "Tasneem nan Gida nane" Mami Matata ce Sai Faizan Yarona ne...

Kin Tuna Na Taba Fada Miki Sunan Yarona "Faizan" Murmushi Tasneem Tai Tace "Ehh Ehhh na Tuna" Faizan Sai Zazzare Ido Yake Kamar Wanda Yayi karya, Har Yanzu Abin Nabashi Mamaki Sosai, Alhaji Ya Kalli Mami Yace "Bayan Na daina Ganinta, Nayi Bincike Aka Fadamin Ta bace, Haka na Cigaba Da bibiyan maganar har Nasake Jin Labarin Tana Wajan Wasu a Cikin Gari...

Tasneem Dai Batace Komai Bah Sai Kallan Alhaji datake Yi, Murmushi Alhaji Yayi Yace "Barkanki da zuwa Gidana" Dan Dariya Tasneem Tai, Alhaji Ya Mike Yace "Hajiya Ina magana" Sama Ya hau Ya shiga Dakinshi, Mami Ta mike Tace "Ina Zuwa"...

Cikinta ne Ya Fara Kugi Ta Janyon plate din Gaban Faizan ta fara ci, Kallanta yayi Ya janye Plate din Yace "Lallai Bakida Kunya Abincin nawa??" Ta Turo baki Tana Shafa cikinta Cikeda Shagwaba Tace "Tho fah Yunwa Nakeji" Ya Harareta Yace "Kinyi Brush neh?"Kara Turo Baki Tai Ta mike Tahau Sama Zuwa Dakinta tana Kunkunai...

Murmushin Farin Ciki Yayi A Hankali Yace "Alhamdulillah Uh Wil Soon Be My Wife Insha Allah" Ji Yayi Abincin Ya isheshi Ya mike Ya dau Wayoyin Shi Ya Fita...

        ***********

Magunguna Dad Ya Amso Ya Dawo Dakin, Mum Ya samu Tana Sallah, Magungunann ya aje Ya fita, Bai Dawoba Sai Chan Yanma Har Lokacin Naeem Bai farka bah, Abinci Dad Ya aje Mata yana kokarin Fita, Ta tareshi Tace "Am Sorry pls, Wallahi its not What you Think" Daga Mata Hannu dad Yayi Yace "I Understand You Dnt hav to Explain" Kofan Ya murda Ya fita...

Zama Tayi Cikeda damuwa Tana Kallan Naeem Kasa Kasa dake Barci Hankalinshi Kwance, Har Dare Bai Farka bah, Budurwan nan Data shigo dazu Ita Ta kara Shigowa Da sallama, Mum Ta amsa Ta dago Tana kallanta, Sannu Tace Mata sannan ta karasa Bakin Gadon Inda Naeem Yake Kwance, Murmushi Tai tana kallan Kyakyawan Fuskanshi...

Stethoscope Dinda ke Wuyanta ta Ciro Ta Samai A Kirji, Saida Ta dudubashi Sannan Ta Kalli Mum Tace "Kiyi Hakuri Mama insha Allah Zai samu sauki, Muna sa Ran Tashin shi Cikin Daren nan" Murmushin Karfin Hali Mum tai tace "Nagode"  Fitowa Tai daga Dakin Tana tafiya Cikeda Jindadi A Hankali Ta Furta "I Love You Naeem"...

Ummu Farheen✌🏻
           N
Aysha Gana💕
[10/10, 3:46 AM] 🍹🍬🛍💍Salma🍷💍🛍🍬: [10/6, 6:10AM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
                  N
         *Aysha Gana*

*129 to 130*

Sterthoscope dinda ke wuyanta ta ciro ta samai a Kirji, Saida ta dudubashi Sannan Ta Kalli Mum tace "Kiyi haquri mama Insha Allah zai Samu sauki, Muna sa ran Tashin shi Cikin Daren nan" Murmushin Karfin Hali Mum tai Tace "Nagode" Fitowa daga tai daga dakin tana Tafiya Cikeda Jindadi A Hankali Ta Furta "i Love You Naeem"...

Karfe Sha Daya Ya Farka mum ta fita dasauri ta kira wani likita Yazo Ya duddubashi Sannan Yace "Ya wanke baki abashi wani Abu Yaci" Mum Jiki na rawa ta dauko brush ta mika mai, Sai mai Sannu Take, Dakyar Ya mike Ya Shiga Toilet, Wanka ya Fara Yi sannan Yayi brush din yayi Alwala, Yana Fitowa Already Ta ajemai Abincin, Yadan Kalleta Murya Chan Kasa Yace "Sallaya Zanyi Sallah" Dasauri Ta Dauko ta Shimfida mai Ya tada Sallah"....

Yana Idarwa Mum Ta ajemai Abincin, Saida Tadingi Mita Sannan Yadanci kadan Ya Ture, Yarinyan Nan ne Ta kara Shigowa da Sallama, Dukansu Suka Amsa Tareda maida dubansu kan Kofan, Naeem na ganinta Yaja guntun Tsaki Ya kauda Kai, Mum Tadan kalleshi Sannan Ta Kalli Yarinyan Cikeda Murmushi Tace "Ya Farka, Nagode Fah Allah Ya saka da Alheri da Lura dashi da kikai tayi" Dan murmushi tai Tace "Bakomai Mama", Mum Tace "Bansan Sunanki Bah?" Murmushi Tai Tace "Sunana Yusrah", Mum Tace "Nafa Gode Yusrah" Yusrah Ta kalli Naeem Wanda Tun Shigowanta Ya kauda kai Tace "Naeem Ya jiki" Yi yayi kaman Baiji bah, Mum Tace "Tanama Ya jiki" Batare da ya kalleta bah Yace "Dasauki" Tamai Murmushi Tace "Allah Kara Sauki" Mum Ta Amsa da Ameen, Sannan Ta Fita...

Naeem Ya hade Rai ya juya Ya Kalli Mum Yace "Mum I hope Baki Bari Yarinyan nan Ta tabani bah" Mum Ta kalleshi da mamaki tace "To sai meh dan ta tabaka??" Ya kara hade rai Yace "Banaso! Pls mum" Murmushi Mum Tai tace "Idan Ance Tabawa daya knan, Ta tattabaka" Naeem Ya juyo Ya Kalli Mum Yace "WHAT?" Mikewa Yayi dasauri Ya Shiga Toilet Wanka Ya Sake Saida Ya gugurje Jikinshi Sosai Sannan Ya fito, Mum sai Kallanshi take abin nabata Mamaki...

Kwanan Naeem Biyu Ya Warware Sosai, Kullum Sai Yusrah Ta shigo ta gaishe da Mum, Likitoci ma haka Saboda Naeem Yadanyi Aiki Dasu Kafin Zuwanshi Nigeria, Ranan Daya Cika Kwana biyu Aka Sallameshi, Dad yazo ya daukesu Suka Tafi Gida, Yusrah Harda Yar Kwallanta Ranan Da Naeem Zaibar Asibitin...

Alhamdulillah Naeem Yasamu Sauki saidai Yanzu ya zama So Silent Magana sam Bai Dameshi bah, Kullum Yana zaune Shi kadai Sai Hoton Tasneem dayake Tasawa a Gaba Yayita Kallo, Wani Lokacin Har Kuka Yakeyi, Dad Ya Fuskanci Halinda Dan nashi ke Ciki, Sannan yayi Alkawarin Koma Wacece Wannan Yarinyan sai Tazama Mallakin Naeem Dinshi...(Tho Pha!)

              **
Faizan ke Driving Sai Baya Mami da Abba Gaba kuma Tasneem, Faizan Yace "Abba Wai Yaushe ne Tafiya Kadunan??" Abba Yace "Ranan Sunday Insha Allah, Saboda mamanka Ta gama Komai nima Nagama" Faizan Yadanyi Murmushi Yace "Allah Ya kaimu" Abba Da mami sukace Ameen, Tasneem Ta juya Ta Kalli Mami Tace "Mami What is Todays Date??" Mami Tace "4th Sept" Menene Baeby?? Zaro ido tai Tace "Mami Gobe Zamu Koma School" Mami tace "Zamu Chanza Gari Zamu Koma Kaduna da zama Sabda Abba Ya samu Transfer Zuwa Chan, Sannan Faizan Yasamu Aiki a Chan, kinga Idan Muka koma Sai Asaki Wani Makaranta Mai kyau Koh" Ihu Ta saki Tana Murna, Faizan Ya kalleta Yace "Kedai Allah Ya Shiryeki" Murguda mai Baki Tai Ta Cigaba Da Murmushi Ita kadai Yayi Kwafa Yace "Zaki Sani dani kikeyi"..

A Bakin wani Babban Boutique Faizan Yayi Parking, Abba Ya Fito Mami Ma ta Fito Sannan Ta budema Tasneem Ta Fito, Turo baki Faizan Yayi Ya kalli Abba Ta cikin Glass din Motan Yace "Ni Abba Baka Budemin Bah" Dan Dariya Abba yayi yace "Oh Faizan Asan An girma dai, Wannan Shagwaban ai sai abarma Tasneem" Kara Shagwabe Fuska Yayi Ya juya Suka Hada Ido da Tasneem Dake Tamai Dariya, Dunkule Hannu Yayi Ya nuna Mata, Ta Kara Kyalkyalewa da Dariya Tamai Gwallo, Abba Ya bude mai Ya fito Sannan suka Dunguma Zuwa Cikin Shagon...

Mami Ta kalli Tasneem Tace "Kuje da Faizan kidau duk abinda kikeso", Tsalle Tasneem Tai Ta Shige Ciki Ta Fara jidan Kaya, Faizan na Bayanta Rike da basket, Inta Dauka Saita Wurga Mai, Wani ya Sameshi a Fuska Wani Ya sameshi a Kirji, Wani a Ido, Wani Ya fadi Ya Dauko, Haka taita wuwurga Mai Kayan Kwafa Kawai Yake Tayi Yana Murmushi Shi kadai,

Saida Ta Jida Kaya Sosai, Faizan na biye da ita dakyar Yake Daukan Kayan, Wajan Teddies ta nufa, Wani Kato Ta janyo, Faizan Yace "Ina zaki kai Wannan gunkin?" Ta Juya ta Turo baki Tace "Inaso ne" Faizan Yace "Tab Gunkin?? Ina!" Bata Rai Tai Tana kokarin Yin Kuka Tace "Ya Naeem Ya Saya min Dayawa Kuma....Bata Karasa Bah Yace "Dauka"Hada Rai Faizan Yayi Sam Baisan Yaji ta ambaci Sunan naeem, Haka Ta gama Jidan Abinda zata jida Suka Fito Abba Ya biya Suka Fito, Har Sun Shiga Mota Zasu Tafi Kamar Ance Tasneem Ta daga ido Tako hango Dr Sa'ad Yayi Parking Yana Kokarin Shiga Cikin Shagon, Tada Motan Faizan Yayi, Tasneem Sai Murda Kofan Take Tana kokarin Fita...

Ummu Farheen✌🏻
           N
Aysha Gana💕
[10/10, 3:46 AM] 🍹🍬🛍💍Salma🍷💍🛍🍬: [10/7, 5:46AM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
                    N
         *Aysha Gana*

*131 to 132*

Har sun shiga mota zasu tafi Kamar ance Tasneem ta daga ido Tako hango Dr Sa'ad Yayi Parking Yana Kokarin Shiga Cikin Shagon, Tada Motan Faizan Yayi, Tasneem Sai Murda Kofan Take Tana Kokarin Fita, Bah Wanda Ya Lura da Abinda Takeyi Har Suka bar Haraban wajan, Saida Suka Hau Titi Sunyi Nisa Sannan Tasneem ta Fashe da Kuka, Faizan Ya Juya Ya kalleta a rude Yace "Menene??" Abba dake Baya Suka Hada baki da Mami Wajan Tambayan tah...

Kasa Magana Tai sai kukan data Cigaba, Har Suka Isa Gidan bata daina Kuka bah, Dakyar ta Yarda Ta fito daga motan, Mami ta kama mata Hannu suka shiga Ciki, Dakyar Ta Fada ma Mami abinda Ke Faruwa, Faizan da Abba nafalo duk Hankalinsu a Tashe, Mami Ta Sauko Tana Fada musu Abinda Tagani, Dogon Tsaki Faizan Yayi Ya Hade Rai, "Shi Harga Allah baisan Ana Maganan Naeem din nan" Mami ta Kalleshi da Mamaki, Baice Komai bah Ya Mika ma Mami Kayan Tasneem din Yabar Falon Dasauri. Abbah Yace "Ai datayi Magana Kinga a Wurinshi Zamu San Inda Naeem din Yake" Mami Tace Hakaneh...

Wuri Tasamu Tazauna Ta Kalli Abba Tace "Dama Akwai Abinda Na Manta ban Fadama bah" Abba Ya gyara zama Yace "Inajinki", Mami Tadanyi Murmushi Tace "Faizan Fah San Tasneem Yake Tuntuni, Tun Bata Nan Gidan Yace "Yana Ganinta a Hanya idan Za'a Kaita Makaranta koh Zasu Fita", Murmushi Jindadi Abba Yayi Yace "Dan Nema Ki Kyaleshi Indai Santa Yake Tho Yazo ya sameni Dakanshi" Itama Mamin Murmushin Tai Tace "Kasan Zai Iya" Abba Yace "Ina Nan ina Jiranshi Saiya zo"...

Yini Tasneem Tai Kuka Mami Bah Irin Lallashin da batai bah Haka Abba sam Taqi Cin Abinci, Sunan Naeem da Mama Laraba Kawai Take Kira, Lokaci Lokaci Takan Kalli Zoben Hannunta da Naeem Ya bata, Abba Ya daga Waya Ya Kira Faizan, Daya zo ya Fada Mai Tasneem Taqi Cin Abinci Sai kuka datake, Dukda Ta batamai Rai anma Sam Baiji Dadin Kukanta bah Dakuma Rashin Cin Abincinta, Dakin Ya Shiga Ya sameta Zaune a kasa ga Abinci a gabanta Ta rungume Hannu sai Kuka Take, Ganin Yanda Idonta Suka kukumbura Yasa Ya Rude Ya Karasa kusada ita Ya zauna, Abincin ya janyo ya Ciro Hankiey a Aljihun shi Ya goge Mata Hawayen, Dagowa Tai Ta Kalleshi Ya girgixa mata kai, Sannan Yace "Pls Stop Crying, banaso naganki kina kuka" Bakisan Kukan nan zai iya jawo miki Ciwo bah?? Pls Stop ko nima Kinaso inyi kukan neh??" Girgiza kai Tai Alamar Aa, Abincin Ya dibo a Cokali Yakai Mata baki Takauda Kai...

Langwabar dakai Yayi yace "Plsssss" A Hankali Ta bude baki Yasa Mata, Saiya Lallabata Sannan Take amsan Chokali Daya, Ahaka Har Tadanci Abincin, Duk Abinda Sukeyi Mami da Abba Suna Bakin Kofa Suna Kallansu Sai Murmushi Sukeyi, Tasneem Ta Kalleshi Tace "Na Koshi" Yace "Are You Sure?" Kai Ta gyada mai Alamar Eh, Ruwa Ya kara bata Tasha, Sannan Yayi murmushi Ya lakaci hancinta Yace "Mai Kukan Banza Kawai" Itama Murmushin tai, Ya mike yace "Ki Shirya Muje Wani Guri" Yana Fadin Haka ya fita Dama Already su Mami sun bar Wajan...

Kaya Tasneem ta Chanza Cikin Wanda Ta zabo dazu, Riga da Skirt Pink Tasa Ta Daura Blue Hijab akai, Kayan sun mata kyau Sosai, A Falo ta Tarar dasu Mami, Dagudu Tai Hanya Fita Sannan Tace "Abba! Mami Mun Fita da Ya Faizan Bye" Mami Tace "Take Care Baeby" A bakin Mota ta Hadu Dashi yana Jiranta, Ya Shiga ita Ta Shiga, Tada Motan Yayi Sannan ya Kalleta Yace "You look Subab!" Murmushi kawai Tai, Ya Kalleta Kasa Kasa Yace "I love You" Dariya tai Tasa Hannu Ta Rufe Fuskanta, Shima Dan Dariyan Yayi yace "Kice Uh Love mie pls" Girgiza kai Tai Alamar Aa Yace "Why?" Kara Girgixa mai Kai Tai, Murmushi yayi Ya Ja motan suka bar Gidan...

Yawo Sukai ranan sosai, Ya nuna Mata Wurare Dayawa, Wani Gurin idan Sukaje Sai tace "Ta taba zuwa Itada Naeem" Tun Tana Kiran Sunan Naeem Yana Bata Fuska Harya Ware Sukai hira Sosai, Kayan ciye Ciye Yasai Mata Dayawa sai Daf da Magriba Suka Dawo Gida Tasneem cikeda Jin Dadin Yawon da Sukai Yau...

 Shirye Shirye Mami Take Sosai na Barin Katsina, Komai Datake Buqata ta dauka Har an Tafi dasu, Sauran Funitures Kuma da Kayan Kitchen Duk Tace "Sa'a Tazo ta daukan ma mamanta" Kayan sawansu Kawai ta hada sai Yan Abubuwan da Ba'a Rasa bah, Rannan Sunday da Sassafe Suka Daga Zuwa Kaduna Garin Gwamna...

Ummu farheen✌🏻
           N
Aysha Gana💕
[10/10, 3:46 AM] 🍹🍬🛍💍Salma🍷💍🛍🍬: [10/7, 2:11PM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
                    N
         *Aysha Gana*

*133 to 134*

Shirye Shirye Mami Take Sosai na barin Katsina, Komai datake Buqata ta dauka Har an Tafi dasu, Sauran Funitures kuma da Kayan Kitchen duk Tace Sa'a Tazo tadaukan ma Mamanta. Kayan Sawa Kawai Ta Hada Nata dana Tasneem saina Abba, Sai yan Abubuwan da Ba'a Rasa bah, Ranann Sunday da Sassafe Suka Daga Zuwa Kaduna Garin Gwamna...

Tun a Hanya Tasneem Tai Barci, Batasan an iso Gariba Saida Suka Shiga Gidan, Jidatai Mota ta Tsaya Yasa Ta bude ido a hankali, Ganinsu Tai a Cikin Wani Hadadden Gida, Haraban Gidan ma kadai Abin Kallo neh, Mami Ta Bude mata Ta Fito Suka Shiga Cikin Gidan, Sakin Baki Tasneem Tai Tana Kallan Gidan, Faizan Ko sai Dariya Yake qasa qasa Ganin Yanda Ta saki Baki Tana Kallo, Mami ta Galla mai Harara bah Shiri Yayi Shiru Yabar Falon..

Mami Ta nuna ma Tasneem Dakinta Wanda Yake Kusada Nata, Ta Shiga Mata da Akwatunan Kayanta Sannan Ta Fito...Kwanansu Biyu Suka Saba da Gidan Already Abba da Faizan Sunyi Resuming aiki, Dukansu Karfe Bakwai Suke Fita Kowa Ya nufi Nashi Gurin Aikin, Mami Dakanta Takai Tasneem Tai Mata Registration a Dambo Intl School Barnawa, Js2 Aka sata Bayan An Mata Exam Taci, Ahaka Itama Ta fara Zuwa Makarantan ta, Abba Yasama mata Driver dazai Rinka kaita Makarantan Yana daukota, Kullum Idan Suka Fita Tasneem Taje Makaranta Mami Kawai Suke Bari a Gida, Drivern Tasneem Tasa Ya cigita mata Yar Aiki Cikin Ikon Allah Tasamu Mai hankali kamar Sa'a Ta cigaba da Mata Aiki...

Tasneem Tayi Sababin Kawaye Yan Gayu Wanda Iyayensu keji da Kudi, Dukda Itama ba baya Take bah, Saboda Abba Na Wadata ta da Sutura Da abubuwan More Rayuwa Iri Iri, A cikin Makaranta Idan Ana Lisafa Yara Masu Ji da kansu Dole Tasneem Tana Cikinsu, Haka Faizan Shakuwa Sosai Ya shiga Tsakaninsu, Har Mami Takanyi mamaki yanda daya ke Damuwa idan bah Daya, Dukda Ita Tasneem Sam Bata Fahimci Santa Yakeba, Shiko Faizan Kokarin Yanda zai Faranta Mata Yake Ya nuna mata Tsantsar Santa dayakeyi...

Wata Ranan Sati Suna Zaune Duka a Dinning Suna Breakfast, Tasneem da Faizan A Plate daya Sukecin Abinci Wannan Yace Wannan Ya Kwashe, Wannan ma yace Wannan Ya Kwashe, Haka Suketa Shirmensu Mami da Abba sai Dariya Suke, Abba yace "Maza Tasneem ki gama kinga Lokacin Islamiya Ya kusa" Tho Tace Suka cigaba daci suna Hira, Maranta ne Taji Ya murda Tace "Ouch!" Dakarfi, Faizan Ya Kalleta Yace "Yaya Whts wrong?" Mami da Abba Suma ita suke kallo, Ta Turo Baki tace "Cikina ke Ciwo" Mami Tace "Bah Dole Yayi Ciwo bah kinata Dura Abinci Bayan kuma kin qoshi, Sai Biyema Faizan kike koh??" Batace Komai bah sai Cije Lebe Datakeyi, A Hankali Ta Mike Rike da Cikin Ta haura Sama Zuwa Dakinta...

Kan Gado Ta Fada Ta Rike Maran Tana Cije Baki, Ciwo Sosai Yake Mata Har Batasan Sanda Ta saki kuka Mai Qarfi bah, Kuka Take Sosai Tana Cigaba A juye Juye Hannunta Riqe da Maran, Tun Tana Kan Gado Har Saida Ta fado Kasa, Mami Ta Hauro zata Shiga Dakinta Taji Kaman Kukan Tasneem, Ta Bude Kofan dakin Kadan Ta leqa, Kwance Tasameta a Kasa tana Juye Juye tana Kuka, Mami ta shiga dasauri ta dago Tasneem A rude tana Tambayanta meya Faru? Kuka Take Tana Nunama Mami Maranta, Dasauri Mami Ta fito Ta Sauka kasa, Faizan Da Abba suna Kan Dinning Har yanzu suna Hira...

Mami Ta Kwalawa Abba Kira a Rude, Tace Kuzo Tasneeeem, Tasneem, Ta koma Sama dasauri, Faizan Ya mike Dasauri Ya haura Saman, Yanda Mami ta barta Haka Suka dawo Suka Sameta Saidai Wannan Karon Bata Motsi, Idanunta a Rufe Sai Hannunta Dake kan maranta, A rude Faizan ya Sungumeta Yayi Gurin Mota da ita, Mami ta shiga, Abba yace "Zan biku a baya kuje" Kuka Mami Take Tana Shafa Fuskan Tasneem Dake Kan Cinyanta, "Faizan hankalinshi a tashe Ya juyo Yace "Pls Mami stop Crying pls" Ya maida Idonshi kan titi, Yana driving Lokaci Lokaci yana bugun Stearing Motan Tareda Cusa Hannunshi na hagu Cikin Suman Kanshi yana Furzar da Iska, A haka har Suka kai Asibitin...

Ummu Farheen✌🏻
         N
Aysha Gana💕
[10/10, 3:46 AM] 🍹🍬🛍💍Salma🍷💍🛍🍬: [10/8, 6:41PM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
                    N
         *Aysha Gana*

*135 to 136*

Faizan Hankalinshi a tashe ya juyo yace "Pls Mami Stop Crying pls" Ya Maida idonshi kan titi, Yana Driving Lokaci lokaci yana Bugun shearing Motan tareda Cusa Hannunshi na hagu Cikin Suman Kanshi Yana Furzar da Iska, A haka har suka Kai Asibitin...

Ko Kwakwaran Parking Faizan beyi bah Ya fito ya bude baya Yadauketa Ya Shiga da ita Asibitin, Nurses neh sukai Saurin Amsan Tah Akai Emergency da ita, Mami a Rude Ta Shigo Ta kalli Faizan Tace "Ina Take?" Dakinda Aka Shiga da ita Ya nuna Mata, Ta Kalleshi da mamaki Tace "Aina Kasamu Jini??" Kallan Jikinshi yayi sai a sannan Ya lura da Jinin daya batamai Riga, Ya kalli Mami a Tsorace Yace "I dnt Knw" Batace Komai Bah, Abba Ya shigo Asibitin, Mami Yasamu Zaune Tayi Shiru, Yace "Ina Tasneem din??" Tace Tana Emergency Har Yanzu basu Fito bah, Sun Dade Sannan Likitan Ya Fito Yamusu Bayanin Period Zata Fara Shine Yazo mata da Ciwon Mara, Likitan Ya kalli Abba Yace "Shawara Anan Alhaji amata Aure da Wuri, Saboda Yawancin Mata Idan Aka musu Aure Suka Sadu da Mazansu Yawanci Suka dena, Abba ya kalli Mami Suka Hada Ido, Yace "Tho Mungode Likita"...

A Kofar Office din Suka Samu Faixan Yadawo Siyan Magani, Ya Kalli Abba yace "Abba meke Damunta" Shiru Yadanyi Sannan Yace bkmai kawai ciwo neh, Duka a Tare Suka Shiga Dakin datake Kwance, Barcinta Take Tasha Sai Drip da ake Kara Mata...

Kwananta Uku a Asibiti aka Sallamesu, Mami Tayi Mata Bayanin Yanda abin Yake, Tasneem Sai Kunya Takeji Mami na Dariya, Kwana Biyu Ta Kara bataje Makaranta bah, A Kwana biyun Ta Ware Sosai Ranan na Uku Ta koma Makaranta...

Naeem ne Zaune a Wani Gurin Shakatawa, Iska ne ke kadawa Mai dadi, Wurin Zagaye da Flowers masu Daukan Ido, Kowa nata harkan Gabanshi, Naeem Koh Kanshi nakasa Hannunshi Rike da Hoton Tasneem Sai Papern Datai Drawing dinta Ita Dashi, Kallan Rubutun Datai a Kasa Yake Yana Kara maimaita Kalmar a Ranshi, Ganin Mutum yayi Ya xauna kusada shi Yadan juya ahankali, Yusrah Yagani Zaune Tana Kallanshi tana Murmushi, Kauda Kai Yayi yaja Tsaki, Tadan Rankafo Tace "Haka Naeem ban Chanchanci Haka daga gareka bah Naeem...

Gyara Zama Yayi Ya juya Baya, Yusrah Ta Marairaice Fuska Kamar mai Kuka tace "Dan Allah Naeem Kaimin Magana konaji Dadi pls" Ina Matukar Sanka Narasa Yanda Xanyi pls karka bari sanka Ya hala Kani, Ya juyo fuska a murtuke cikin Fushi Yace "Ya halakaki Mana So What, I Hate You Yusrah, I hate You! Ki Fita Daga Rayuwana mana Dole ne Saina Soki nace Bana sanki, Ki Barni Naji da Abinda ke damuna pls" Yana Fadin Haka Ya mike Yabar Wajan...

Fashewa da kuka Yusrah Tayi ta bishi da Kallo harya Bace, Drivern daya Kawoshi Ya Tukashi Zuwa Gida, A Garden Yasamu Dad Yana Hutawa, Har xai Wuce dad Ya kira Sunanshi, A Hankali ya Taka Har zuwa Inda Yake, Dad ya nuna mai Kujera Yace "Sit" Bah Musu ya zauna kanshi a kasa, Dad Yayi gyaran murya Yace "Lokaci Yayi Naeem dazaka Cire Komai a Ranka, Bana Jin Dadin Ganinka haka, Munyi Magana Da Management din Hospital Din nan Sunce Ran monday ka Koma Aiki, Tunda dama kai ka gujesu, Naeem Ya Dago dasauri Yace "Butttt...

Dad Ya Katseshi yace "Shhh! Banasan Musu Naeem, I promise You idan Har Ka Koma Aiki Sannan ka Cire duk wata damuwa a Ranka, Ni dakaina Zanje Nigeria na nemi duk Inda Tasneem Take i Promise, And She Wil Insha Allah be Your Wife", Naeem ya dago Fuskanshi Dauke da Murmushi Yace "Dad are You Serious??" Dad Ya gyada kai yace "Nataba Maka Wasa??" Naeem Ya mike ya rungume Dad Yana Dariyan Farin Ciki Yace "Thank you dad! Thank You, You d best dad Ever" Ya sakeshi Ya Shiga Cikin Gidan a Guje Yana Kwallawa Mum Kirah...

```To Fans ya kuke Ganin Mum Zatai reacting Idan Taji Wannan Zanchan??```

Ummu Farheen✌🏻
           N
Aysha Gana💕
[10/10, 3:46 AM] 🍹🍬🛍💍Salma🍷💍🛍🍬: [10/9, 9:00AM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
                    N
         *Aysha Gana*

*137 to 138*

Naeem ya dago fuskanshi Dauke da Murmushi Yace "Dad are you serious??" Gyada kai Yayi Yace "Nataba Maka Wasa?" Naeem Ya mike Ya Rungume Dad Ydba Dariyan Farin Ciki Yace "Thank you dad! Thank You, You d best dad Ever" Ya sakeshi Ya Shiga Cikin Gidan a guje Yana Kwallawa Mum Kirah...

Tana Daga daki tajiyo Kiran Naeem, Yanda Yake kiranta Alamar da Alamar Farinciki Yasa Ta Tashi Dasauri Ta tari dan Nata, Tana Fitowa Sukai Kicibus Yana Kokarin Shiga, Murmushi Ya Sakar Mata Ya Rungumeta, Turus Mum Tai Yaushe Rabonda Koh Murmushin Naeem Tagani, Itama Murmushin Tai Tace "Tel me Son meya Faru??" Yadanyi Dariya  Ahankali Yace "Mum dad Promised me Idan na Fara Xuwa aiki zaije Nigeria Ya nema min Tasneem" Murmushin Murna Mum Tai dan Ta Gaji da Ganin dan nata a Wani Hali, Yanzu ta Yarda Sosai Naeem Yakesan Tasneem, Mum Ta shafa Suman kanshi Tana Murmushi Tace "Am Very happy, Allah Yasa Rabon muce" Naeem Yace "Ameen Yabar Wajan Cikeda farin Ciki...

Tun Daga Ranan Naeem Ya Saki jikinshi Yadawo Naeem dinshi nada, Ranan Monday da Sassafe Ya Shirya Cikeda Farinciki Zai Tafi Asibiti, Mum Tayi Tayi Ya Tsaya Yaci Abinci Anma Ina! Haka Ya tafi Asibitin. Doctrs da Nurses harma da Cleaners Sunyi Murnan Ganinshi Sosai Ciki Harda Yusrah dake ta Kokarin Nuna Mishi Murnan ta Yana Sharewa, Haka Ya Cigaba Da Aikinshi Kullum Sai Yusrah Ta dameshi...

Sati biyu da Komawan Naeem aiki, Dad Ya karbi address din Garinsu Tasneem a Wajan Naeem, A Sati na Uku Dad ya Dau Hutu a Wajan aiki ya taho Nigeria. Har Airport Naeem ya raka dad Saida Yaga jirginsu ya tashi Sannan Ya koma Asibiti...

Naeem ne zaune a office dinshi Yana duba Foldern Wani patient, Knocking Yaji a Kofan, Yace "Yes come in" A Hankali ta murda Hannun kofan ta Shigo, Bai Dago bah Ya cigaba da Abinda Yakeyi, Jin Shirun Yayi yawa Yasa Ya Dago kai, Yusrah Yagani Tsugune a Kusa Dashi idonta taf da Hawaye, Ya hade Rai Yace "What dah hell are you doing in my Office" Hawayen Dake Maqale a Idonta Suka zubo, Tace "Naeem ina Azabtuwa da Sanka, Dan Allah karka bari sanka ya zama Ajalina Dan Allah, Ina Sanka ina matuqar Kaunarka. Ta Fashe da Kuka mai Tsanani Kanta a kasa, Kauda Kai Yayi Yadanyi Tsaki, Ta dago Tace "Kasoni koda Rabin wanda nake maka neh Dan Allah"...

Ya Mike Dasauri Tareda Buga table dinda ke Gabanshi Yace "Yusrah Get out of my Office Now!" Ta kalleshi da Mamaki, Yace "Out pls i dnt Want to see you" Ta bude Baki zatai magana Yace "Getout I Said" Wani Likita ne ya shigo dasauri, Dan Naeem dakarfi yake maganan Har saida Asibitin Ya dauka, Ganin Naeem ne da Yusrah Yasa Yace "Oh! Sorry pls" ya fita Daga Office din...

Naeem Ya Kalli Yusrah Ya nuna Mata Hanyar Kofa, Tafiya tafara yi Tana Waiwayen Naeem Har Tabar Office din..Tsaki Yayi ya juya Tana Kallan Window, Dagudu Yaga Yusrah ta fito Tahau motanta Ta Fita a guje daga Asibitin, Shiru Yayi Sai kuma Yaji Baiji Dadin Abinda Ya mata Bah, Zama yayi yanajin duk bah dadi, Anma idan ya tuna Abinda Dad Yaje yi Saiya Tsinci Kanshi Cikin Farinciki...

A Nigeria Kuwa Dad Ya Isa lapia, Bayan kwana biyu Dad ya shirya ya nufi Gangara, Address dinda Naeem Yabashi Yabi Har Cikin Kauyen, Wajan mai Gari aka Rakashi, Sun gaisa Sannan Dad Yamai Bayanin Zuwanshi, Mai Gari ya cika da mamakin Kalaman Dad, Yace Sam Tasneem bata dawo bah, Yanzu kuna nufin kuce ta bata??? Dad Yamai Bayanin duk Yanda Abin Yafaru, Mai Gari hankalinshi ya Tashi Sosai...

Dad ya bada Haquri Sannan Yayi alkawarin Insha Allah Zaisa Abi gidajen Radio da Tv a nemeta, Sai A sannan Hankalin Mai Gari yadan Kwanta (Kunsan mutumin kauye) ya Musu Alheri Sosai Ya baro Kauyen, Kwana Uku Ya Kara ya Koma China, Ranan daya Koma Naeem dakanshi Yaje Ya dauko dad daga Airport, Koda Naeem Yaji Labarin Yanda abin Yakasance baice komai bah, Chan Ya kalli dad da idanunshi dasuka Cika da Kwalla yace "Nagode da Kokarinka" ya Mike Yabar Wajan...

Tun daga Ranan Naeem Yaxama abin Tausayi Yakoma Kamar Yanda yake Kwanakin Baya, Mum da dad na Matukar Tausaya mai, Bah ma Kamar Mum, Asibitin ma bakoda Yaushe Yake Zuwa bah, Kullum Yana Chan Bakin Ruwa Yana Kallan Yanda mutane Kowa Ke Harkan Gabanshi cikeda Farin ciki da Annashuwa....

*Bayan Shekara Biyu*

Gagudu ta Sauko daga Stirs din tana kwallawa Mami Kirah, Mami dake Falo kan Kujerah Tace "Gani nan Baeby" Ta karasa ta fada jikin mami Tana dariya Tace " dagaske Abba Ya biya mana Makka??" Mami tai Murmushi tace Dagaske Mana Duka Tare Zamu Tafi but banda Faizan, Ta bata fuska Tace "Saboda meh Mami??" Murmushi tai tace "Sunqi Yarda su bashi Hutu a wajan aiki" Tasneem ta Shagwabe Fuska tace "Nima tho bazan je bah" Mami ta zaro ido Tace "Saboda Faizan Bazashi bah??" Kai Tasneem ta gyada Daidai da Sallaman Faizan, Suka amsa Tasneem ta mike dasauri Ta tareshi Tace "Uh welcome bro" Brieafcase din Hannunshi ta Amsa Tana mai murmushi, Shima Murmushin Yake yace "Thanks Honey! Ya lakaci Hancinta Ya Sassauta murya Yace "Har Yanxu baki fadamin bah" Ta kalleshi Tace "Mene?" Ya Kwaikwayin Muryanta Harda yanda tai da baki Yace "Baki cemin kina sona bah" Dan Dariya Tai Tabar Wajan dasauri. Kokarin binta yake Mami Tai gyaran Murya Tace "Tho Mara kunya Gani nan"....

Ummu Farheen✌🏻
             N
Aysha Gana💕
[10/11, 9:03 AM] 🍹🍬🛍💍Salma🍷💍🛍🍬: [10/11, 6:01AM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
            N
    *Aysha Gana*

*139 to 140*

Ya Kwaikwayan Muryanta Harda Yanda tai dabaki Yace "Baki cemin kina sona bah" Dan Dariya tai Tabar Wajan dasauri.
Kokarin Binta yake mami tai gyaran murya tace "Tho Mara kunya Gani nan" Sosa keya Yayi Yace "Sannu Mami ai banganki bah" Tadan Harareshi "Dama Ya za'ayi kagani, Kadai Kama Girmanka sannan Abbanka Yace "idan Har dagaske kake sai kaje ka fadamai dakanka" Kurri Yayi yana Kallan Mami da Mamaki "Ya akai Yasani??
`Ni nafada mai ko bakyau neh??
Girgiza kai Yayi ya mike "Lemme take shower, Mami am very hungry"
yana Fadin Haka yabar falon Zuwa side dinshi...

Duk suna Zazzaune kan Dinning Suna Dinner, Faizan Yadan Kalli Abbah "Abbah Yaushe zaku tafi?" Dan Murmushi Yayi Sannan Yace "Ka kosa mutafi neh??" Kai Ya girgiza Alamar Aa, Abba Yace "Kaduna Ba'a fara tashi bah Kasani, Anma Ya kalli Mami Yace "Ku Zauna Ciki Shiri"
`Tho Tace, Tasneem Ta Aje Chokalin Ta zumburo baki, Abbah Ya kalleta Yace "Tho yar rigima na menene??"
`Abbah Meyasa banda Ya Faizan??
Kallanta Faizan Yayi Cikeda Mamaki, Ashe Tasneem tadamu dashi. Dad yace "Ya miki bayani mana Shi. Murmushi Faizan Yayi ya Kashe mata Ido Daya, Itama Murmushin Tai, kurrri ya mata Yana Kallanta, Duk abinda Sukeyi Mami na Kallansu, Ganin basuda Niyan Gamawa Tace "Idan Kun Gama Kalle Kallen da Murmushin ai Sai ku miqe koh??

Kunya ce Ta rufe Tasneem Ta Tashi A Guje Tabar Falon, Dakinta Ta shiga, Kagado Taga Sabuwar waya Kirar "Samsung Galaxy grand prime" harda Sim. Sai Wata Yar paper da aka rubuta "```4 uh my Tasneem Sai Chan Kasa Aka rubuta i love You kasa kuma akasa Faizan!```

Murmushi Tai tadau Kwalin Ta ciro Tasa a Chaji, Sai washe gari zata School ta Tuna, Mami Ta nuna Mawa Tace "Ya Faizan ne Ya saya mata" Mami Tace "Iyeh Allah Ya Saka da Alheri anma kuma banso kika riqe Waya yanzu bah, Kinga Ss1 kike akai Sauran 2yrs a gabanki Tasneem Banso Waya ya dauke miki Hankali" Turo Baki Tai, Mami ta amsa wayan Tace "Tho Iya rigima adawo lapia" Dasauri Ta fita ta shiga Mota Driver Yajata Zuwa Schl...

A bakin Gate ta Hadu da Frnds dinta Raleeya da Fatee suma anyi Droping Dinsu, Dariya sukaima Juna suka Shiga Schl, Saida Ala tashi Break Take Fada Musu Maganan Zuwa Makkanta da Kuma Sabuwar Waya da Ya Faizan ya saya mata, Sun Mata Murna Sosai, Fatee Tace "Ni Sai nake ganin Kamar Faizan din nan sanki yake" Dukan Cinyan Fatee Raleeya tai tace "Abinda zance knan Yar uwa kika Rigani" Tasneem Tace "Kullum Sai Yacemin Yana Sona Wai Nima Saina Cemai" Raleeya Tai Dariya Tace "Kicemai Mana So What?? Koh ke bakya sanshi??" Fatee tai Saurin Cewa idan Bakya sanshi ni Wallahi ina Sanshi, Gayen Ya hadu ga iya daukan wanka..

Hade Rai Tasneem Tai Ta Kalli fatee Tareda Mikewa Tace "Tho sai kije ki Aureshi" Barin Wajan tai Ranta a bace (Meh Tasneem take nufi?? Na tambayi kaina...)
Bata Kara musu magana bah har aka Tashi, Suko Sai dariya suke mata, Rai Bace Ta koma Gida, Tambayan duniya Mami tai Mata anma Taqi bata amsa Akarshe ta Fashe Da Kuka....

Dad Ya kalli Mum Yace "Nagama arranging Komai nida Naeem zamuje Saudi arabia Yaga ka'aba Ko Yasamu Sassauci" Mum Tace "Haka Ma yayi daidai" Naeem me Yayi Sallam Ya shigo Kanshi a kasa(nayi matuqar tsorata Ganin Yanda Naeem Ya rame Gwanin ban tausay!)
Dakinshi Ya hara Dad Ya kira Sunanshi, Tsayawa Yayi batare daya Juyoba Yace "Ka Shirya next week zamuyi tafiya" Baice komai bah Yayi Shigewar shi daki, Kuka Mum Ta Fashe Dashi Tana Cewa "Duk nina ja wannan abin Yanzu ji yanda dana Ya koma, Ya Allah ka baiyana Mana Tasneem" Dad Yace "Ameen Ya isa pls banasan Kukan nan, Bah lefinki bneh Haka Allah ya tsara Ki Daina Kuka...

Ummu Farheen✌🏻
            N
Aysha Gana💕
[10/12, 11:33 PM] 🍹🍬🛍💍Salma🍷💍🛍🍬: [10/12, 8:26PM]









💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
                N
        *Aysha Gana*

*142 to 143*

Kai Tasneem ta gyada tana murmushi dai dai nan Naeem ya Shigo Wajan Fuskarshi Dauke da murmushi, Gabanshi ne Ya fadi Ya riqe kirjinshi A hankali Bakinshi Ya Furta "Tasneem" Waige Waige Ya soma Yi, Mutane ne Cike a Wajan Kowa na Harkan Gabanshi, Kara Shiga Wajan Yayi Yana  dube dube...

Tasneem ko Addua Sukaima Mamatan Dake kwance a Maqabartan, Mami Tace "Sai Muje koh??" Noqe kafada Tasneem Tai ta Kalli Abbah tace "Nidai Muje Shopping" Murmushi Abbah Yayi yace "Tho Muje Sarkin Rigima" Abbah Natafe Mami da Tasneem suna Binshi a Baya Har Wajan Maqabartan, Mai Taxi suka Tare Suka Shiga Daidai Nan Naeem Ya fito Daga Maqabartan, Idonshi Suka Sauka akan Tasneem data Shiga Motan Tanama Abbah Dariya, Dagudu Yayo Wajan Motan Anma Kamin Ya iso Har Motar Tabar wajan...

Gudu Ya soma yi yanabin Motan Ganin Gudun bazai Fidda shiba Yasa ya Tari Mai Taxi ya nuna mai Motan Yace Yabisu, Tafiya suke Sosai Su Naeem sai bin Motansu Tasneem Yake, Su Abbah Na Wucewa Go Slow ya Hadu a Wajan dole Motar da Naeem Take Ciki Ya tsaya, Nooo! Naeem yace Tareda Dukan Murfin motan, Koda Go Slow din Yayi Sauki Yawo sukaita yi Har Yanma, Ganin Yanma tayi Yasa Naeem Yacema Mai Taxi Ya kaishi Gida...

Shopping Sosai Tasneem Tai, Tun daga kan Abbah har Mami da Ya Tasiu Sai Naeem da Gogan Nata Faizan, Mama Laraba ma Bata Barta bah, (Niko Ummu Farheen Nace Ko aina zata gansu tabasu Oho) Itama Tasai Nata Kayan Sosai Tareda Kawayenta Na Schl, Mami Ta saki Baki Tace "Duk kayan nan Ina zaki kaisu??" Turo baki tai tace "Tho Fah Mami kowa da nashi Kayan, Girgiza kai Kawai Mami Tai Tana dan Dariya, Niki niki Da Kaya suka dawo masaukinsu Tasneem Ta Hada Kayanta a akwatinta Sannan Ta kwanta...

Dad Ya matukar Tsorata Ganin Yanda Naeem ya dawo, Dasauri ya Riqeshi yana Tambayanshi Meya Faru, Murya Chan Kasa Naeem Yace "Dad Naganta anma Ta tafi" Dad Yace "Wah??" Tasneem dad naganta dazu itada wasu, Shiru Dad Yayi Yana Kallansh da mamaki, Anya Naeem bai Tabu bah?? Baice Komai bah ya Kwantar dashi Kan Gado Tareda Tofeshi da Adduoi A hankali barci mai Nauyi ya daukeshi...

Alhamdulillah su Tasneem an Gama Aikin Hajji Ranan da suka Diro kasa Nigeria Da Faizan Ta fara Arbah, Murmushi Suka Sakarma Juna, Koda Suka Dawo gida, Komai na Gidan ab Chanza bama kamar dakinta, Abbah Yace "Kayi qoqari Faizan Allah Ya Saka da Alheri" Ameen Faizan Yace Tareda Murmushi. Washe Gari Tasneem ta Fito da Tsaraban Kowa ta bashi, Kaya Sosai Tasaima Faizan, Godiya Yayi sannan Yace "How Did you knw my Size" Batace Komai ba dan Ita Harga Allah Irin Size din Ya Naeem tasaya mai Kuma Tasan Tana Fdamai Irin na Ya Naeem ne Zasu bata, Kara Tambayanta yayi, Tadan Langwabar dakai Sannan Tace "Mami Ta Fadamun"...

Yadan Harareta Yace "keda Mijinki Bakisan Size dinshi bah??" Ta Turo Baki Ta mike Tabar Wajan, Yace "zan Kamaki neh" Juyowa Tai tamai gwallo Tabar Wajan a guje...

Kwananta Uku da dawowa ta koma Schl, Frnds dinta na School sunsha Tsaraba Sosai, Tasneem Ta maida Hankalinta Gurin Karatu sosai, Soyaiya Suke Sosai Itada Faiza Dukda Ita Har Ynzu bata Yarda Sanshi Takeba Kuma bata Taba Fadamai bah, Anma Duk wanda Yagansu Yaga Yanda suke Tattalin Juna Yasan Suna San Junansu...

A kasar China kuwa Labari Yasha Banban, Naeem ya koma Kamar bashi bah, Abin Har Tsoro Yasoma bah Mum da Dad, Addua Sukasa Agaba Bah Dare bah Rana Cikin Ikon Allah Hankalinshi Ya Fara dawowa Gareshi, Ya Rage Tunani Sosai, Yana walwala Fiye da da dukda Kasan Zuciyarshi Tasneem dinshi na nan Maqale, Ya Cigaba da zuwa Aikinshi dama Tuni Yusrah Tabar Asibitin...

*Bayan Shekara daya*

Sanye Take da Atamfa Green da Ratsin Fari, Hannunta Rike da Handbag na Versace, Flat Shoe ne a Kafanta Shima Green, Yarinyan Ta matuqar tafiya da Imanina, Saida na Qura mata ido Sosai Sannan Na Gane ashe Tasneem ce, Faizan neh Ya Fito rike da Car key dinshi Yace "Am Sorry Bae" Turo baki Kawai tai Batace Komai Bah, Ta shiga Motan Ya tada Suka bar Gidan, wayanta ne Ya soma Ringing Ta Dauka tana murmushi, daga chan Bangaren Akace "HBD Frnd! Sai munzo Cin Cake" Dariya Tadanyi tace "Tho Kwadayaiya Sai Kizo kici" Itama Dariyan Tai Ta Kashe wayan, Faizan Kaman Ya Mata Magana ya fasa, Tafiya Suke Tayi Batare datasan inda Suka Nufa bah, Ganin tafiyan Yaqi Karewa Yasa Ta Kalleshi tace "Wai ina Zamune??" bareda ya kalleta bah Yace "Sai dake Zanje nayi"

Shiru tai Batakara Cewa komai bah, Sunyi tafiya Mai Nisa, Motan Ta fara Cijewa, Ganin Taqi yasa Sukai Parking, Faizan Ya fito Ya bude Gaban Motan, Hayaqi ne ya furzo Yadanyi Tsaki ya Daki motar da Kafanshi, Tasneem ta Fito Tace "Whats Wrong Ya Faizan" Kai yayi Magana Wani Daga bayansu Yace "Alhaji Tsayawa Taine??" Ni meh Gyara neh Barin Dubah mah, Zaro Ido Tasneem Tai ko a Mafarki taji Muryan nan bazata tabah Manta Maishi bah, Dasauri Ta juyo Suka Hada Ido Tace ....


Shin Masu Karatu Wah Tasneem tagani??

Ummu Farheen✌🏻
           N
Aysha Gana💕
[10/14, 7:46 PM] 🍹🍬🛍💍Salma🍷💍🛍🍬: [10/14, 1:33PM]




💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
                  N
        *Aysha Gana*

*144 to 145*

"Whats Wrong ya faizan??" Kan Yayi Magana Wani Daga Bayansu Yace "Alhaji Tsayawa Taine??" Ni Mai Gyara neh Barin Dubah mah, Zaro ido Tasneem tai ko a mafarki taji muryan nan bazata tabah manta maishi bah, Dasauri ta juyo suka hada ido Tace *Ya Tasiu!!!*, Da Mamaki Yake Kallanta, Fashewa Dakuka tai Ta matso kusada Shi Tace "Ya Tasiu nine Fah Tasneem, Baka ganeni baneh??"..

Idonshi Cikeda Kwalla Yace "Tasneem Kece??, Ina Kika Shiga Inata nemanki" Ta kara rushewa da kuka ta juya ta kalli Faizan daya Tsaya yana kallansu Tace "Ya Faizan Wannan Shine Yayana" Murmushi Yayi Ya miqama Tasiu Hannu sukai musabaha, Murya chan Kasa Tasiu Yace "Wanene Wannan??" Cikeda Jindadi Tace "Labari neh Mai Tsawo" Kazo muje gidan mu, Karasawa Yayi Barin Motan Ya dudubah, Sannan Yace "Tayar mugani" Bah musu Faizan Yashiga ya Tayar, Tasiu Ya rufemai Gaban Motan, Faizan Ya fito Yace "Dan Allah Kabimu muje Gidanmu, Yakamata Kasan Inda Qanwarka Take Rayuwa, Kuma Nasan Akwai Tambayoyi Fal a Ranka da kake Buqatar Amsar su" Shiru Tasiu Yayi Ya Kalli Tasneem Ta gyada mai kai tana Share Hawaye, Ya Kalli Faizan Tareda Murmushi Yace "Shiknan Muje" Kayan Aikinshi ya kwasa yasa a Motan Suka juya Suka nufi gida...

Tun a Hanya Faizan Ya kira Mami Yamata Bayani, Cikeda Murna Tace "Sai Kunzo" Yace Tho Mami Tareda Kashe Wayan, Cikin Mintina Kadan Suka isa Gidan, Tsayawa Kallan Gidan Tasiu Yayi Cikeda Mamaki, Sai Kalle Kalle Yake kamar Bakauye, Tasneem ta riqemai Hannu Ya Kalleta Tamai Murmushi Suka Shiga Falon, Mami ce Ta taresu da Fara'a, Har Kasa Tasiu ya Tsugunna Ya gaida Mami, Murmushin jindadi Tai Ta amsa, Kallanshi Ta Tsaya Yi Cikeda Mamaki, nuna mai Kujera tai Dakyar Ta bude Baki Tace "Ga guri Zauna Ina Zuwa"  Tho Yace Ya zauna, Tasneem ta zauna kusada shi tace "Ya Tasiu!" Murmushi Yamata Yace "Na'am Tasneem" meh Kikeyi Anan??...

Ta fadada Murmushi Tace "Ya Tasiu Kasan meh??" Girgiza kai Yayi Yace "Fada Inaji" Tace "Shekaran nan naje Makka" Zaro Ido Yayi da Mamaki Yace "Dagaske??" Hannu Tasa a Jakanta Tace "Bari kagani" Wayanta ta dauko ta shiga Hotuna, Hotunan Data dauka a Makka ta nuna mai, Cikeda Mamaki Yace "Alhamdulillah Burinki Ya cika" Duk da bansan Mutanen nan bah Anma Naji a raina Mutanen Kirki ne Allah Ya Saka musu da Alheri Riqeki da sukayi...

Mami Ta sauko Cikeda Fara'a Tace "Tasneem ina Faizan??" Tace "Ya fita Bansan Inda Yaje bah, Horn Suka Ci na Motar Abbah, Dagudu Tasneem ta Fita ta Taroshi Tana Fara'a, Tare Suka Shigo Falon, Mikewa Tasiu Yayi Cikeda Ladabi, Abbah Ya karaso wajanshi Yace "Barka da Zuwa, Ina Cikin Farin Ciki Yau da Allah Ya nuna min wani na Tasneem" Dagowa Tasiu Yayi Yana Murmushi Suka Hada Ido, Gabanshi ne Ya Fadi Ganin Fuskan Tasiu, Ya juya Ya kalli Mami, Itama Shi Take Kallo Ya kara Juyowa Ya Kalli Tasiu, Gani Yayi Ya Tsugunna Har Kasa Ya Gaida Shi, Amsawa Abbah Yayi a Daburce, Ya Kalli Mami Yace "A bashi daki Sannan Yaci abinci anjima Inaso mu zauna duka" Yana Fadin Haka Yabar Falon Ya haura Sama zuwa dakinshi...

Mami Ta fadama Tasneem Dakinda Zata Kaishi, Suka Mike Tana Riqe da Hannunshi Har dakin, Har Yanzu Kallan Tasneem Yake cikeda Mamaki, Abinci Ta Kawomai Ta Fita, Sai Bayan Isha'i Abbah Na Falo Shida Mami..

Fsizan ne Ya Shigo da Sallama, Mami Ta Harareshi Tace "Ka kyauta ina Kaje Tin dazu" Murmushi Yayi ya Hada Hannayenshi Yace "Sorry Mum! Wani abokin aikina ke aure yau Shap na manta" Batace komai bah, Tasneem Ta sauko riqe da Wayanta, Abbah Yace "Jeki ki kira Yayanki" Tace Tho Ta nufi dakin Dasauri, Mami Tace "Kaima zauna Akwai Maganan da Za'ayi" Bah Musu Ya zauna, Tasneem ta Shigo Falon da Sallama Tasiu na Biye da ita...

Wuri suka Samu Suka zauna kusada Juna, Mami tadanyi Dariya Tace "Baebyna yanzu anga Yaya An Daina Zama Kusa dani koh??" Murmushi Kawai Tai, Abbah Yayi Gyaran murya Yace "Munaso Musan Labarin ku ina Nufin daga Inda Kuke, Menene Asalinku?? Sannan Ina Iyayenku Suke", Mami Tace Kafin Nan Inaso Tasneem ki bama yayanki Labarinki Tun Bayan Rabuwanku, Murya a Sanyaye Tasneem Ta bada Labarin Rayuwarta Tun Tafiyan Tasiu Har Zuwa Ranan, Saida Tagama Ta Share Hawayenta, Shima Tasiu Kukan Yake a Hankali...

Mami Tace "Komai Ya wuce Yanzu kai Muke Saurare" Tasiu Yadan Dago Ya kallesu Sannan ya Fara Kamar Haka..

"Mahaifinmu Dan Asalin Jimeta ne Adamawa State, Sunanshi Alhaji Aminu Sabo, Sai Mahaifiyar mu Fatima ita Kuma Yar Maradi ce Kasar Nijar" Abbah Ya Mike Dasauri Yana Kallanshi Yace "What???"...

*Ina Fatan Zakumin Afuwa Kwana biyu banida Lapia neh shiyasa banyi Post bah, Stl ina Baran Adduan Ku*

Ummu Farheen✌🏻
         N
Aysha Gana💕


[10/15, 6:00AM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
                   N
       *Aysha Gana*

*146 to 147*

"Mahaifinmu dan Asalin Jimeta ne Adamawa state, Sunanshi Alhaji Aminu Sabo, Sai Mahaifiyarmu Fatima Ita Kuma Yar Maradi ce Kasar Nijar.
Abbah Ya mike Dasauri Yana Kallanshi Yace "What??"
Itama Mami Miqewa Tai Tace "Lapia Alhaji maiya Faru??"
Kallan Tasiu Abbah Yayi Sosai Yace "Tabbas Hakane, Dukda Banji Labarinka bah anma Masan Kai Dan Alameen neh Ga Kama"..
Cikeda Rashin Fahimta Tasiu ke Kallan Abbah, Zama Yayi Sannan Yace "Ina Alameen??" Yana Ina Yanzu??
Mami Ta Kurama Abbah Ido Tace "Alhaj kila fah Sunan neh Kawai Yayi daidai Kabari Ya cigaba da Fadamana, Baice komai bah Mami ta Kalli Tasiu Tace "Muna Jinka"

`Na Taso Nikadai ne Gurin Mahaifina, Sai Mahaifiya tah, Muna Adamawa akamai Transfer Muka koma Minna da zama, Na Tashi Cikin Gata Gurin Mahaifina, Tunda Nake Ban taba Ganin wani na Mahaifina bah, Harda Mahaifiya Tah, Duk sanda na Tambaye shi sai Yace min Yanada Yaya Sunanshi "Jibrila" kuma Zai Kaini Karna Damu, Ita Kuwa Mahaifiyata Bana Tambayanta Saboda Nasan Tayi nisa da Kasarsu, Ina Aji Uku na Sakandiri Mahaifiyarmu Ta Fara Rashin Lafiya, Koda Akaje Asibiti aka Gwadata Sai akace Tanada juna biyu..

`Haka muka Cigaba da Rayuwa Yau Ciwo gobe Lafiya, Kullum Mahaifina baya nan Yana Gurin aiki, Nike Lura da Ita Har Tadan ji Sauki sannan nacigaba da xuwa makaranta nah, Bana Manta Wata Ranar Sati da misalin Karfe Bakwai na dare ina zaune a dakin mahaifiyata inacin Abinci mukaji Hayaniyan mutane a Gidan, Da mamaki muka Fito, Ashe aure ya qara batare da Mahaifiyata tasani bah, Hakan Bah Karamin Kona Mata Rai Yayi bah Anma Ta danne Bata Fadamai Bah...

Shiru Yayi tareda Fashewa da kuka, Tasneem ta dafashi Itama kukan Takeyi, Mami ce Tai Karfin Halin Cewa, Kai Haquri duk abinda kagani ya faru da dan Adam dama muqaddari ne daga Allah, Saida Yayi Mai Isarshi Sannan Ya Cigaba dacewa..

`Haka Ta cigaba dazama Cikin Rayuwar Qunci da Tsangwama, Kullum Mahaifina Bashida Abu sai hantara Da Tsangwama, A Haka Har Allah Ya sauketa Lapia, inda Aka Samu Tasneem, Tanada Shekara Uku Lokaci na Kammala Secondry dina, Wata Ranar Laraba Nadawo Daga Makarantar Islamiya harna Cire Kayan Islamiya nah Naji Mahaifina na kwallawa Mahaifiyata Kira, dasauri ta Karasa Kusadashi, Ya mika Mata Takarda Yace "Banaso na Qara Ganinki a Gidan nan Ki Tattara inaki inaki kibar gidan nan"...

Da Mamaki na leko Daga dakinmu Ina Kallanshi, Yana Ganina Yace "Karta Sake Tabar Mai ko Yaro daya duka Ta hada Ta Tafi damu" Kuka nafara ina Bashi hakuri, Ko Kallona Beyi bah Ya Shige dakin Amaryar Sah, Ina Hangota Tana Leqomu ta window Tana dariya, Mahaifiyarmu Sai Kuka Take, A Haka muka kwashi Kayanmu Muka Bar Gidan...

Shiru Yayi Yana Goge Hawayen Fuskanshi, Tasneem Dake Gefenshi ko kuka Wiwi, Itama Mami Sai matsar Kwalla Take, Abbah yace "Me yakaiku Karin Katsina??" Tasiu Ya Gyara Zama Yace;

`Mun Bar Gidan Batareda Musan inda xamu nufa Bah, Tasneem Tana Bayan Mahaifiyarmu a Goye Sai Kuka Take, Da Kafa Muka kai Tasha Batareda Mun Sani bah, Ji kawai Tai Conductor Na Ihun "Katsina!" Ta Kalleni Tace Mushiga, Ban Mata Musu bah Nashiga Mota ta cika Mukadau Hanyar Katsina, Tun a hanya Ta Fara Rawar Sanyi, Na kalleta A sanyaye Nace "Mama Bakida Lapia neh??" Kai Kawai ta iya Gyada Min, Sai Chan Cikin Dare muka Isa Katsina, Mun Fito Tasha Muka Rasa Inda Xamu Nufa Ga hadari Daya Hadu a Garin..

Bakin wata Itaciya Muka Zauna, Anan xuwa Yayimana Duka Ranan Washe Gari, Da Zaxxabi Mahaifiyarmu Ta Kwana Tana Rawar Sanyi Sosai, Na Rasa Yanda xanyi duk Wanda natara Nace Ya taimaka Mana saiya Gudu Har Yanma, Cikin Ikon Allah, Allah Ya Jeho Mana Mallan Ado Shiya Kaimu Gidanshi Muka Cigaba da Rayuwa Harna Tsawon Shekara Biyu Sannan Allah Yadau Ran mahaifiyarmu...

Kuka Sosai tasneem ta Saki Tace "Ya Tasiu Mamanmu Ta Rasu?? Kai Ya Gyada Shima Yana Kukan, Mami data dafe Kirji Tace "Innalillahi Wa inna ilaihi Rajiun, Kana Nufin Fatee ta Rasu??" Faizan ya kalli Mami da Idanunshi da suka Rune Yace "Mami Kinsanta neh??"kantai Magana Abbah Ya Dauka Muryanshi na Rawa Yace "Alameen Qanina meh Uwa Daya Uba Daya" Dukansu Suka Juyo Suna Kallanshi da mamaki...

Ummu Farheen✌🏻
           N
Aysha Gana💕


[10/15, 2:03PM]

💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
                  N
       *Aysha Gana*

*148 to 149*

Faizan Ya kalli Mami da Idanunshi da suka rune Yace "Mami kin Santa neh??" Kantai Magana Abbah ya dauka Muryanshi na Rawa Yace "Alameen Qanina neh Uwa daya Uba daya" Dukansu suka Juyo suna Kallanshi da Mamaki, Kai Ya gyada Alamar Eh Sannan Yace Kwarai kuwa, Mu biyu Iyayenmu Suka Haifa, Nine Babba Sannan Alameen, Tun Bayan Rasuwan Iyayemu Muka Rabu Saboda Wani Abu daya Faru a Tsakaninmu..

Mikewa Yayi ya haura Sama Chan Sai Gashi Rike da Wani envelop ya mikama Tasiu Yace "Bude Kagani" Bah Musu Ya amsa Ya bude, Hotuna neh Suka Zubo Yadau Daya Yaduba Sannan Ya maida Dubanshi ga Abbah Dasauri Yace "Kwarai Kuwa Wannan Shine Mahaifinmu" Mami Tai Murmushi ta daga Hannunta sama Tace "Allah nagode maka Yau Gani ga Yayan Fateema," Ta Kalli Tasiu Tace "Mahaifiyarka Mutumiyar Kirki ce, Nima Nan daka Gani Yar Nijar ce, Fateema Yar uwace Agareni, Nayi Kukan Rashinta Daga Baya Nabarma Allah komai Inda Rabon Zamu Gana..

Mun Rabu da Fateema Lokacin Tanada Cikinka, Allah Be nufa Zamu qara Haduwa bah, Mami Ta fashe da kuka Tace "Allah Ya jikanki Fateema Allah ya Gafarta Miki, Duka falon Suka Amsa da Ameen, Faizan Yace "Yanzu idan mukaje Minna xaka gane Gidan,? Girgixa kai Yayi Alamar Aa, Mami Tace  "Ina Ai bazai Iya ganewa bah Shekaru neh Fah Masu Yawa"...

Cikeda Damuwa Abbah Yace "Allah ka nunamin Dan Uwana Alameen, idan Yana Raye, Idan kuma bai Raye Allah ka Jikanshi da Rahama, Na Yafemai Duk abinda Yamin Duniya da Lahira" Dukansu Suka amsa da Ameen, Dadine Ya kama Tasiu Sosai Yau Gashi ga Wan mahaifinshi, Abbah Yace "Kana Makaranta neh??" Gyada Kai Yayi Yace "Ina 400lvl yanzu, Da kanikancin danakeyi nake Samu inama Kaina Abubuwa" Abbah Yace "Allah Saki" Allah yamaka Albarka, Yace "Ameeen"

`Daga Rana Irinta Yau Ka dawo gidan nan, Duk wani abu da dan Gata Akemai, Ko yake Mallaka Insha Allah xanyi Kokarin Yimaka Shi, Daga Yau ka tashi daga Maraya Insha Allah, Godiya Sosai Tasiu Yayi Yana Matsar kwalla, Faizan da Mami Suka tayashi Godiya...

Cikin Sati Daya Tasiu Ya murje Sosai, Kyanshi da Tsantsar Kamarshi da Tasneem Ya Fito Sosai, Cikin Yan Kwanakin Sunyi sabo da Faizan Har Yake Fadamai Abnda ke Ranshi gameda Tasneem, Dadi Sosai Tasiu Yaji Yace "Insha Allah shi zai Shigemai Gaba Wajan Maganan auren", Godiya sosai Faizan Yayi, Yana Cikin Satinshi na Biyu Abbah Ya Bashi Mota Kirar Toyota "Corolla S", Bah Karamin dadi Tasiu yaji bah Yar kwalla Yayi, Tasneem Ta Taya Yayanta Godiya Harda Mami da Faizan, Ana Haka Hutunshi Ya Kare Ya Koma Makaranta, Duk Weekend Yakan Dawo Gida...

Bayan Wata Shidda

Ya Tasiu dan Allah Kai Sauri Kagafa Yau Zamu Fara Exam ko so kake nai Latti, Kara Dukan Kofan Tai, Yadan Leqo Tareda Hade rai Yace "Keh Bazanfa Jeba Kije driver Yakaiki" zumburo Baki Ta nufi kitchen inda mami Take, Mami Tana Ganinta Tace "Tho Baebyna Waye Ya Tabamin keh??" Idonta ne Ya ciko da kwalla Tace "Koh bah Ya Tasiu bneh wai Bazai Kaini Makaranta bah, Shine Harda Dungureni, Mami Tace "Dunguri??" Kai Tasneem ta Gyada Dai dai da Shigowan Tasiu kitchen din Yace "Oh na dungureki koh??" Dasauri ta boye bayan Mami Tace "Nifah bah Haka nace bah" Ya xaro ido da Mamaki yace meh kikace?? Shiru Tai, Kokarin Nufota Yake mami Tace "Ah Tasiu agabana,"

`Mami Wallahi Yarinyan nan batada Kunya, Wai Yanzu a gidan nan Sai Wanda Tazaba Zai Kaita Makaranta, Duk Faizan ne Yadaure mata Gindi Take abinda Tagadama, Mami Ta qara Karesta Tace "Tho yi Haquri yanzu dai Jeka Shirya kaxo ka Kaita" Dasauri Tace "Aa Mami Wallahi Nafasa Banaso" Hararanta Yayi Tareda Gwafa Yace "Dayafi miki" Yana Barin Gurin Ta Fito daga Bayan Mami Tace "Natafi Mami" Allah Ya kiyaye Mami Tace Tana Murmushi..

Ranar Wata Lahadi, Tasneem Ta tashi da Ciwon Mara Kamar Yanda Tasaba duk wata, Wannan Karan Yafi na Kowanne, Dakyar Ta Mike Ta nufi dakin Mami Riqe da Maran nata, Mami na Ganinta A rude Tace "Lapia??" Maranta ta nuna Mata, Mami Ta Karasa Tareda Riqeta Tana Mata Sannu, Haka Suka yini Har Gurin La'asar, Ganin Tasoma Fita Haiyacinta Yasa Mami Ta sauko da A Rude Ta Kwallawa Faizan Kira, A Tare Suka Fito Tareda Tasiu, Mami tace "Tasneem Zaku kamamin Mukaita Asibiti, Nan Da nan Faizan Yarude Yafi mah Mami, Dagudu Ya haura Rama xuwa dakinta, Ganin Bata Nan Yasa Ya fito Ya shiga na mami..

Kwance Yasameta Tana Birgima Akan Gado, Tasiu da Mami Suka Shigo atare, Daukanta faizan Yayi Ya nufi Wajan Mota da Ita, Tasiu na Biye Dashi, Yana sata A Mota Ya zagaya Ya Shiga, Tasiu Ya shiga Gaba, Mami Ta Shiga Baya Suka nufi Asibiti, nurses Na Amsanta Sukai emergency da ita, Daya daga cikinsu ta tafi Dagudu dan Kiran Doctr, Bude Kofan Office Din Tai a Hankali, Yana zaune Yana rubutu a Cikin Wani File, Batareda ya Kalleta bah yace "Any Problem??" Nurse din Tace "Akwai Emergency neh Sir! and Its Critical" Mikewa Yayi ya gyara suit din Jikinshi Yadau Stethoscope Yace "Follow mie with BP Machine" Tace "Ok Sir!
Tana Biye Dashi Har Kofan Dakin, A Hankalin ya murda Kofan Ya Tura Kai...

Ummu Farheen✌🏻
           N
Aysha Gana💕


[10/19, 10:45 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
                  N
      *Aysha Gana*

*150 to 151*

Daya Daga cikinsu ta Tafi Dagudu dan Kiran Doctr, Bude Kofan Office Din Tai a Hankali, Yana Zaune yana Rubutu a cikin wani File, Batareda ya Kalleta bah Yace "Any problem?" Nurse din Tace "Akwai Emergency neh Sir! And its Critical" Mikewa Yayi Ya guara Suit din Jikinshi Yadau Stethoscope Yace "Follow mie with BP machine" Tace "Ok Sir! Tana Biye Dashi Har Kofan Dakin, A Hankali ya Murda Kofan Ya Tura Kai, Mutuwar Tsaye Yayi Yana Kallanta, Yakai Kusan Minti Biyar a Tsaye Har Saida Nurse din Tace "Sir!" Rintse ido Yayi Yace "Excuse mie" Aje BP machine din tai Ta Fita, Karasawa Yayi Gurin Gadon Yana Kallanta Kwalla Cike a Idonshi
`Tasneem Dama Zan Ganki??'

Ganin Abin yake kamar a Mafarki, Marin Kanshi Yayi Yaji Zafi, Hakan Ya tabbatar mai daba Mafarki Yake bah, Hawaye ne Suka Gangaro Daga Idonshi, Ya goge Yasa Hannu a aljihun Shi Ya ciro Wayanshi, Wani Number Ya Kira Ana Dauka Yace "I nid Ur Help in Emergency Room 3" Bai Jira maizaice bah ya Kashe Wayan, Chan Saiga Likitan Ya Shigo, Bayani yamai Ya fita, Likitan Ya dudubata Yareda mata duk wani abinda Yakamata, Sannan Ya Je Office Din Naeem Yamai Bayani...

`Baiyi Mamaki Bah, Yama Likitan Godiya, Shiru Yayi yana Tunani na kusan mintina Sannan Ya mike Dan Ganin Wayanda Suka Kawota..

A Waje Kuwa, Mami da Tasiu harda Faizan Sunyi Chirko Chirko a Reception suna Jirah, Mami Ta Kallesu Tace "Kusamu Guri ku Zauna" Bah musu sukai Gurin Kujeru Zasu Zauna, Wata Matace Ta Shigo asibitin da Kuka Tana Kokarin Shiga Cikin Wards din, Zabura Tasiu Yayi Cikeda Tsoro, Bin Matan Ya soma Faizan na kiranshi, Baiko Saurareshi Bah Har Yakai Bakin Kofan Dakin...

Wani dattijo ne kwance daga gani kasan Yanajin Jiki, Dasauri Tasiu ya karasa Cikin dakin Faizan na biye dashi, Ya Karasa kusada Gadon Idonshi Cikeda Hawaye, Matarce Tai Magana Tace "Bah inda Banje Neman Temako bah, Anma Bansamu Komai Bah" Share Hawayenshi Yayi Yabar dakin Dasauri, Faizan Yayi Saurin Taranshi Yace "Bros lapia Whts Wrong" Muryanshi a Sanyaye yace "Shine Mahaifinmu" Da Mamaki Ya kalli Tasiu, Ya Karasa wajan Mami Dasauri Ya mata Bayani Ya kira Abbah Shima Ya gayamai, Mami Cikeda Doki Tace "Ina Tasiu??" Yazo ya nuna mana Dakin...

Bah Inda Faizan Bai dubah bah Anma bah Tasiu, Ya kira Wayanshi Yanata Ringing bai Dauka bah, Yace "Mami muje Nasan Dakin" Suna Shiga Mami Taganshi Tace "Shine" Wallahi Shine, Matar Ta Kalleta Da mamaki Tace "Shine wah??" Idon Mami ya ciko da Kwallah Tace "Meke Damunshi??" Matsar Kwalla ta soma Tace "Tyhoid ne wai ya Tabamai Hanji, Dole sai anmai Aiki Mu kuma Bamuda Kudin", Shiru Mami Tai Tana Kallanshi, Daidai nan Wayan Faizan Ya soma Ringing Yana Dauka Ya fita Chan Sai Gashi da Abbah...

Yana Shiga Ya karasa Kusada Gadon Dasauri Hawaye Cike a Idonshi Yace "Alameen, Bude idonka Ka gani, nine Yayanka Jibrila" Dan Motsi Yayi ya Bude ido ahankali, Yana Ganin Abbah Ya fashe Da kuka Yace "Jibrila Ashe xan kara ganinka??" Dan Allah Ka Yafemin, Nasan nayi Maka bah daidai bah, Hannu Abbah Yasa ya Rufemai Baki Yace "Bakaga Bakada Lapia bah" Ya kalli Faizan Yace "Kaje kaima management din Asibitin Magana Yanzu ai arranging a Shiga Dashi Surgery konawa neh Zan Biya" Faizan Yace Tho Ya fita Dasauri, A bakin Kofan Sukai Kicibus Da Naeem tareda Wata Nurse, Ta Kalli Naeem Tace "Taredashi Aka Kawota" Naeem Yace "Ohk Thank uh n uh can lyv" Dasauri tabar Wajan...

Faizan Ya Kalli Naeem Hankali Tashe Yace "Doctr meke Faruwa da Sister nah??" Ya dake Yace "Ok kaika Kawo Wannan Patient din??" Gyada kai Faizan yayi, Naeem Yace "Menene Sunanta??" Bah Bata Lokaci Faizan Ya fadamai, Naeem Yace "Pls inada Magana da Yan uwanku, I mean Your Parents, its a very serious issue", Kallanshi Yayi da Mamaki Yace "Doctr fadamin meya Faru??, pls Karka Fadamin Labari mara Dadi, Dan Murmushin Karfin Hali Naeem Yayi Yace "Dnt uh worry bah Komai" Ya Nuna Dakinda Su Abbah suke Ciki Yace "Our parents are inside" bah tareda bata lokaci bah Naeem Ya shiga Dakin...

Cirko Cirko Yasamesu a Tsaye Sai Patient din dake Kuka kamar Ranshi zai Fita, Faizan Yama Abbah da Mami Bayani, Naeem Yace "Meet me in My Office", Yana Fadin Haka Ya Fita Dasauri, Faizan ne Yayi saurin Binshi su Abbah da Mami na Biye dashi Har office din, Guri Ya nuna Musu Alamar su Zauna, Bah musu Suka Zauna, Shiru ne Ya biyo baya Na Kusan Minti Uku, Dakyar Naeem ya Furzar da Iskan bakinshi yace "Sunana Dr Naeem" Asalina Dan Jahar Katsina Meh, Nayi Matuqar Mamaki dana ganku da Tasneem Shine Nakeson Qarin Bayani, Tsaki Faizan yayi Yace "Wht Nonsense nama Dauka Wani abu neh, Ohk Ynzu Kana nufin Saceta mukai Or What??"...

Kallanshi Naeem Yayi da Mamaki Yace "Dnt Joke With me and am nt Talkng To uh, Da Parents dinka nake" Yunkurin Magana Faizan Yake Abbah Yayi Saurin Dakatar Dashi Yace "Banso naqara Jin Maganarka Faizan" Fita Yayi Daga Office din Tareda Banko Kofan" Abbah Yace "Kayi Tambaya mekyau Kuma Banga Lefinka bah" Tasneem Yarinyata ce, Babanta Qanina neh. Shi kaganmu Taredashi a Dakin nan Baida Lapia, Naeem Yace "Kai Hakuri, Bah ina nufin Wani abu neh Shine Yakasa fahimta na" Mami Tace "Bkmai Dama duniya ya gaji Haka, Kaine Naeem dinda Take bamu Labari knan tayi zama Wajanka" Naeem yayi murmushi yace "Nine, Na dade ina nemanta" Mami Tai murmushi Tace "Tho Yau Gashi Allah ya nuna maka ita" Ya mike Yace "Muje Ku Ganta"..

Duka Suka miqe Suna Biye Dashi Har Dakin, Barci suka Sameta Tanayi, Mami Taima Naeem bayanin Laluran Mahaifin Tasneem, Yace "Bah Bangarena baneh anma Insha Allah Zanyi Duk Yanda zanyi" Mami Da Abbah Sukamai Godiya Sosai Ya Fita...

Ummu Farheen✌🏻
           N
Aysha Gana💕
[10/19, 10:45 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 💥💥TASNEEM💥💥

Na *Ummu Farheen*
                  N
       *Aysha Gana*

*152 to 153*

Duka suka miqe suna biye dashi har dakin, Barci Suka Sameta tanayi, Mami Taima Naeem Bayanin Laluran Mahaifin Tasneem, Yace "Bah Bangarena baneh anma Insha Allahu Zanyi Duk Yanda zanyi" Mami da Abbah Sukamai Godiya Sosai Ya Fita, Abbah Ya kalli Mami Yace "Yaron nan Yanada Hankali" Murmushi Mami Tai Tace "Nima Sam banga lefinshi bah Dan Yayi Wannan Tambayan", Abbah Yace "Ina Zuwa" Ya fita Daga Dakin...

Naeem keta Kaiwa da Komowa Har Ranan Har aka Gama Arranging Theatern daza'ama Babansu Tasneem, Daidai Za'a Tafi dashi Tasneem Ta farka, Mami tagani Kusada Ita, Mami Tai Mata Sannu Tareda Mata Albishir din Ganin Mahaifinsu, Dirowa Tasneem Tai Daga Kan Gadon Tace "Mami Ina Yake??" Mami Ta Rike Mata Hannu Har Dakin, Likitoci Tagani Gurin Uku a dakin Sunata aunashi, Ta Karasa Kusada Gadon Murya Chan Kasa Tace "Baba" idonshi a Rufe da Alama Barci Yakeyi, Naeem ne Ya Shigo Dakin Sallama, Dasauri Tasneem ta juya Suka Hada Ido, Murya Na Rawa Tace "Ya Na...Naeeem!" Murmushi Yamata Yana Kallanta Da Narkakun Idanunshi, Kurri Ya Mata Yana Kallanta Ganin Yanda Ta Girma Ta kara Tsawo, Komai Ya zauna a Jikinta, Ta karaso Kusadashi Tareda fashewa da Kuka Tace "Ya Naeem inata Nemanka Ina Kaje??" Hancinta Ya Lakata Yace "Har Yanzu kina nan da Kukanki koh"..

Murmushi Tamai Yasa Hankiey Ya Goge Mata Hawayen Yace "Kuka Ya kare Kinji Stop Crying" Murmushi Ta kara Mai dai dai nan Faizan Ya Murda Kofan Dakin Ya Shigo, Ganin Naeem na Gogema Tasneem Hawaye Yasa Ya bata Rai Yana Kallan Mami, Girgiza mai Kai Tai, Huci Yake Kamar Zaki Ya Karasa ya Janye Tasneem daga Wajan Yace "Dnt Uh Evr set ur Stupid Hands on My Sistr" Da Mamaki naeem Ya kalleshi...

Tasneem Ta Kwace Rikonda Faizan Yamata Tace "Ya Faizan Baka Ganeshi bneh??, His my Brother also, Naeem ne fah, Wanda Kake Ganinmu Tare Years back", Tsawa Ya daka Mata Yace "Shut up" Karna Kuskura Naqara Ganinki Dashi, Mami Ranta a Bace Ta Kalli Faizan Tace "Get Out of dis Room now Mara Mutunci Kawai" Hararan Naeem Yayi Tareda Kwafa Yabar Dakin, Da Kallon Mamaki Tasneem Tabi Faizan Harya Bar Dakin, Mami ta kalli Naeem Tace "Pls kai haquri Kasa...Kanta Karasa Naeem Yayi Saurin Katseta Yace "Bkmai" Ya maida Dubanshi ga Tasneem Tareda Murmushi Yace "Am Happy to See uh again My Love" Dariya tadanyi Tareda Rufe Fuska..

An Shiga Theater da Babban tasneem, Harda Naeem Aka Shiga, Tasneem Na Dakinda Aka Kwantar da ita Sai Addua Take Tana Hawaye, Saida Tagama Ta kalli Mami tace "Banga Ya Tasiu bah" Mami Tace Dazu fah Yana Nan Bansan Inda Yaje Bah, Tasneem Batace Komai Bah Ta Kwanta Kan Gadon Ta qudundune, Faizan Koh Figan Mota yayi Yabar Asibitin, Gida Ya koma Ya Shiga Dakinshi, Anan yasamu Tasiu Kwance Idanunshi a Rufe, Ya kalleshi da Idanunsh dasuka rune Yace "Tasiu Dama Gida Kadawo??" Tun dazu nake kiranka baka dauka bah, Shiru Yayi Baice komai Bah, Ganin bai amsa bah Yasa Yayi tunanin koh Barci Yake dan Haka Ya Shige Ban Daki dan Watsa Ruwa...

Awa Hudu Cur Suka dauka a Theatern Abbah na Bakin kofan Yana Sama da Marwa Tareda Adduoi, Naeem ne Yafara Fitowa, Abbah Ya kalleshi Yace "Yaya" Murmushi Naeem Yayi Yace Karka damu Insha Allah Komai Ya wuce" Abbah ya riqe Hannun Naeem Yace "Nagode Allah ya Saka da Alheri" Ameen Naeem Yace Aka Fito dashi aka Kaishi Dakinda Yake, Abbah Ya leka Dakinda Tasneem take Yace "Hajiya kizo an Gama, Wai Ina Matarshi Tundazu Banganta bah" Mami Tace "Nima Kamar zan Tambayeka" Tasneem ta sauko Tabi Bayansu Har Dakin, Naeem ya Shigo Ya Chanza Mai Drip Yace "Muna Sa ran Farkawanshi Nanda Mintina Kadan" Tasneem Ta Kalleshi Tareda Murmush Tace "Thank Uh Ya Naeem" Shima Murmushi yamata, Mami Tace "Tho Itafa Wannan Patient din naka??" Dan Dariya Yayi Yace "Itama zata iya Tafiya Zan Rubuta mata Magunguna dazatasha" ...

Maganin Ya fita Yasiyo Mata Yakawo, Mami Tace "Alhaji Bari Muje Gida Mudawo koh" Abbah Yace "Wai ina Faizan neh??" Tabe Baki tai Tace "Bani Makulin motanka kawai muje Gida" Naeem Yace "Mami in Bazaki damu bah Muje Nakaiki, Abbah Yace "Yauwa Shiknan ma Kuje nikam Bazan bada Motata bah" Duka Dariya Sukai, Naeem da Tasneem sukai Gaba, Yace "Naganki da Waya Gv me ur numbr" Fadami Tai Ya Rubuta Yace "I Missed You Soo very Much My Love" Tai dan Dariya Tace "Mie Too" Yace "Sure??" Kai ta gyada Mai...

Hannunta ta daga tana Gyara Gyalen kanta Yace "Uh Kept ur Promise" ta akalleshi Cikin Rashin Fahimta Yace "Yea Baki Cire Ring dinda nabaki bah" Hannun Ta kalla tai dariya daidai nan Mami ta karaso wajan...

Dasauri Ya bude Motan Mami Ta shiga Sannan Tace "Thank uh" Tasneem Ta Shiga Yajasu, Mami namai kwatance Har Kofar Gidan, Daidai Nan Faizan Ya fito dasauri Dan Zuwa Masallaci Yagansu, Tsaki Yayi Ya Wuce...

Ummu Farheen✌🏻
           N
Aysha Gana💕

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *