Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Tuesday, August 27, 2019

Bibiyata Akeyi Complete (dandalin hausa novels)

adsense here
Bibiyata Akeyi Complete (dandalin hausa novels)
Compiled by Umar Dalha.

. BIBIYATA AKEYI         

Bismillahirahmanirrahim

Writing by
            _Zaynab Bawa (z33iiyyb3rw3r)_

Page 1

Zaune take acikin wajan amma hankalinta baya jikinta domin kana kallanta kasan tana cikin matsananciyar damuwa wanda hakan yagaza boyuwa sanda yanuna akyakyawar fuskarta,

 Tunani take acikin zuciyarta shin ko tajene tasamesu taji dalilin wannan *bibiya* da takura dasuke mata ne, atake wata zuciyar tayi saurin gargadarta domin batasan mugaye bane,

Amma aida mugaye ne dasun dade da cutar dake, wata zuciyar tace da ita. Mtswww taja wani dan siririn tsaki, ni wallahi tsoronsuma nakeji tafada cikin muryar kuka tareda kifa kanta ajikn table dinda yake gabanta.





Tosu wayannan mutanen suwaye?? mesuke nema awajanta??? Wani laifin tamusu dasuke *bibiyar*rayuwarta?? dataga dai bata dayadda datasamu amsar tambayoyinta kawai tamike tare da zarar jakarta tayi hanyan fita daga restuarant din dake cikin school din zuwa hall na lectures dinsu tana kallo daya yayiwa daya mZ33yyb3rw3ramu nuna masa ita yayi akan tatashi subita koda taga haka wuff tafice daga cikin wajan batareda datsaya biyan kudiba dan damuwa bata barta tayi ordering  komaiba

Koda tafita tayi noticing ana binta amma hakan be daga mata hankalinta dan abunyafara binjiknta direct hall dinda zasuyi lectures tawuce tasamu har malamin sunshiga sa'arta daya bame tsanani bane yasa tayi saurin shiga tasamu gefen kawarta amira tazauna

Amira rada tamata akunne ke inata kiran phone dinki ina kika shiga kikabari phone anata kira banza ainaso kiyi missing attendance,

Gabaki daya wannan surutun da amira takeyi batasan atakure dakeba kawae tatashi tacanja wajen zama tace kici kanki

Ana tashi kuwa ko takan amira batayi ba tafice dama shine last lecture dinsu na ranan,                kodatafita batayi mamakin ganinsu ba don tasan za'a rina (wae miji ya saki mata ubansa yaje zauranci)
Fita tayi tawuce gida koda tana keke napep ma haka taga suna binta sanda tazo dab shiga gida kafin suka juya,

Tana shiga gida tasauke wata nauyayyan ajiyan zuciyarta,
Da sallama tashiga tasamu babansu harya dawo tatsuguna aladabce tamasa sannu da hutawa ya amsa cikin sakin fuska sannan tatashi zata tafi harta fara tafiya naji yace, *hanna*

*Hanna*ni unknown nakara maimata sunan araina nace amma sunan yayi saurin juyowa tayi  cikin ladabi da nitsuwa tace na'am baba yace idankin shiga ciki kyakiramin mamanki toh tace tareda juyawa

Tacigaba da tafiya cikin nutsuwa giftawa tajeyi taji wani zancen daya hargitsa mata Tunani yakara gigitata tare da tsundumata cikin damuwa kunnenta takara kawowa kofar dakin taji hajiyah lami wacce suke kira da Amma tanacewa,

Ai aikin malam nakarangi yanakyau kiduba tun yarinyannan naarama danasa yatura mata aljani wadda ze hanata aure aizancen danake miki haryau bbu wanda yataba sallama da sunan yazo wajanta ga yan uwanta komai ya kankama biki kawae muke jira itakuwa shiru kikeji kamar an aiki bawa garinsu tana gama fadin haka suka tafa tareda shekewa da wata shedaniyar dariya aibata jira sunkara wata maganar dazata daga mata hankaliba tawuce jiri na ebar ta harshirin yasadda ita yakeyi

Tana shiga dakin mamansu kawae tafada kangado tasaki wani marayan kuka me tsuma ran me sauraro

Temakonta daya mama bata dakin yasa tayi kukanta mai isarta daganan tatashi tawanke idonta daganan taadauro alola tayi la'asar tayita addu'o in neman tsari daga sharrin mutum da aljani

Mamane itada inna kaltu mai aikinsu Zaune akicin tana dafawa baba ruwan shayi ni inna kaltu kuwa kinga diyarki tadawo daga makaranta

Najita shiru haryanxu batazo tacemin tadawoba inna kaltu take aikwa bangantaba inaga bata dawoba, to halan cewar mama dauke da gajeruwar damuwa aranta

Yarone dan kimanin shekaru 12 yayi sallama mama waekije inji baba yana falo yana jiranki toh kace masa ganinan zuwa

Fita tayi daukeda farantin ruwan shayi ahannunta tanufi falo anan tatarar da baba yana karanta jarida sallamarta ce tasashi ajiyewa tareda zare gilashin dake idonsa amsa sallamar yayi sannan takaraso ciki   tazauna tazuba ruwan shayin tamika masa yakarba yadan kurba sannan yayi gyaran murya mama tajuya ta fuskanceshi dan da'alama maganar dayakesonyi mai mahimmanci ne

Shin waini halima meyake damun diyarkine gabaki daya ina lura da ita kwanannan batasakewa batada walwala shin meke damunta?? Hmm wani gauron numfashi taja wallahi alhaji nima kwanakinannan haka nake kallonta narasa meke damunta nifa alhaji inaji yarinyar nan dagaske fadan mutanenne halan aljanine ya aureta

Kul karnasake jin wannan zance abakinki baba yayi saurin gargadarta ni inaji aji kina wani alkhairi ne yake BIBIYAR RAYUWARTA kace mahaifiyarta keyakamata kije kiji damuwarta

Bayan ta idarda sallah ne taki shingida tafara gyangyadi tagakamar inuwar mutum akanta agigice tafarka ta............

Shin wae wayake BIBIYAR rayuwar *hanna*??????????

Shin wae Su wayannnan mutane dasuke BIBIYAR yaruwarta ta suwayene???????

Shin dagaske Aljanin da aka turo mata ya sameta kuwa ko akwae wani boyayyen al'amari ne

Domin samun amsar wannan tambayoyi kubiyoni musamosu tare

Ur's
     Z33yyb3rw3r

BIBIYATA AKEYI         

Bismillahirahmanirrahim

Writing by
                _Zaynab Bawa (z33iiyyb3rw3r)_
         

Page 2
*
Gani tayi kamarda inuwar mutum akanta agigice tafarka lokaci daya kuma tasauke ajiyar zuciya ganin mama dake tsaye akanta,

Sunkuyar da kanta tayi sannan tace sannu dashigowa Mama batareda ta amsa taba tasamu waje tazauna sannan tace *hanna* ta dago takalleta cikin sanyin murya tace na'am mama,

Meyake damunki kifadamin dan banasan kallonki cikin damuwa murmushin yake ta kirkiro sannan tace bbu komaifa mama mekika Gani shiru mama tayi tazuba mata ido tana nazarin yanayinta ta kunsan uwa da danta koyaya dah yakai da boye damuwarsa takan gane yana cikin damuwa

*hanna* sunanta da mama takira ne yasata dago kanta daga sunkuyen da take sannan tace na'am mama tadaura da cewa nimahaifiyar kice kina tunani idan baki fadamun damuwarkiba akwae wanda yacancanta kifadawa bayanni

Murmushin yake takara kwakulowa sannan tace Allah mama bbu komai kainane yakemin ciwo kuma gashi samester yazo tsakiya karatu yafara zafi

To Allah yasauwake kisha magani saikihuta mama tafadi hakane bawae danta yarda cewa yartata bata da wata damuwa ba, kuma bawae dan tanada tabbacin datasha maganinba

Mama nafita tasauke ajiyan zuciya tareda jawo alqur'ani taci gaba da karantawa nantake taji kashi tamanin daga cikin dari na damuwarta ya gushe damuwarta ta batafi saura kalilanba

Rufe qur'anin tayi sannan tanade pray mate din cikin natsuwa tanufi kofar       Fita daga dakin

================

katafaran masarautace mai girman gaske
Wanda ko bantsaya muku bayaniba kunsan yanayin girman masarautar kano dan tana daya daga cikin masarautu masu girman gaske
A wannan kasa tamu masarautace mai yawon jama'a

Da dumbin alkhaire atattare acikinta wanda kuma tasamu adali jajirtaccen sarki dattijon  arziki mai farar aniya

*Sarki*Abdulaziz lamido

Wata mata nahango zaune akatafaren falon sarki wanda yasha kayan alatu dana more rayuwa matar dake zaune afalon kana kallonta koba'afada ba kasan itace matar sarki domin ko daga yanayin kayan dayake jikintama zainuna hakan balle azo zuwa yanayin fatar jikinta

Dukda dai bawata walwala atare da ita amma hakan baihana kyawun fatarta futowa kallo daya daka mata kagane damuwar dake tattare afuskarta

Ahankali tasa gefen gyalenta tamatso kwalla sannan tace mai martaba badai kanaso kagwadamin bani na haifeshiba shiyasa kaki amincewa da kudurina amma kasan yanda nake sansa araina koh yayan dana haifa bana sonsu haka

Kasan yadda nake jinsa araina kuwa  tafada cikin muryar kuka inajin ciwo acewae shekara 35 amma haryanxu yagagara yin aure kuma munzuba masa idoh muna kallonsa

Nifa wannan yarinyar daya damu da ita atunanina aljanace ba mutum ba, mai martaba yakura mata ido kawae domin bayaso yatsaida ita saita dasa aya

Sannan taci gabada cewa tayaya xa'ace shekara tara kenan kullum zancensa mutum daya bamusanta bamutaba kallontaba

Mai martaba baza'aduba wannan zance ba idan da'abi shawarata atara malamai kawae suyita masa rokon Allah har adace wannan aljana tarabu dashi

Gyaran murya mai martaba yayi sannan yace bawae naki tatakiba amma yakamata mujira harsai shekatunda ya eba mana suncika kafin muyanke masa hukunci

Ainida ba se anjira ba dan wannan ba mutum bace ga yar uwarsa intisar aisai ahadasu

Kilishi Kilishi Kilishi mai martaba yakira sunanta tareda hadaerai sannan yace

Nafada miki alkawari na dauka zanbarshi yacika wannan lokacinda ya eba donhaka banasan sake jin tashin maganar nan

Toh tace amma bawae dan ranta yasoba sannan tatashi tawuce zuwa shashinta

Tana Fita fadawa sukafara kwasan gaisuwa amma ko kollonsu batayiba tawuce dayake Kilishi Allah yayita mace mai girman kai dakuma nuna isah

================

Zaman cikin gidanne yasoma gagararta domin sai habaice habaice kawae akeyi

Koda Mama taji abinda Su Amma sukeyi hakan baisa tatanka musu ba dan inda sabo tasaba kuma Allah yayita mace mai hakuri wanda gane fushinta abune mai wuya

Juyarda kanta tayi wajan inna kaltu sukacigaba da aikinsu domin yau itace mai girki domin bata taba bari mai aiki tayi ma mijinta abinci itata keyin kayanta

*Hanna* tashi tayi tayi da niyar shiga daki Hafsat da rabi'ah wanda suke yayu a wajanta ne suka tafa tareda shekewa da dariya Hafsat tace dama wasukam Ai saidai Zaman daki domin ba mashin shini suka kara tafawa yoh saima kunbata bakinkune kewar amma aixaman daki yanxu akaafarashi

Zuruf *hanna* tashige daki domin itama kanta abunyana damunta wani irin bakin jinine dani tafada tareda fashewa da matsanancin kuka

Amma yau tasamowa kanta amsar tambaya tada dade tana addabarta aranta, aljanine dagaske ya aureta tunda da kunnan ta taji bawani bane yajimata

Toh sukuma wayannnan masu *bibiyarata* suwaye shin ko suma aljanune??? ta tambayi kanta

Wannan tambayarne haryanxu takasa samun amsar ta kuma batasan wazata nema ya amsa mataba

Saidai takudirta aranta bawanda zaiji wannan zancen
Ai idan aljani yafi karfinta Toh itama akwae wanda zata kai karansu wajan sa

Tadauki alkawarin yin tsayiwar dare tahana idanta barci harsai Allah yamata sakayya da wayannan azzalumai masu BIBIYAR rayuwar ta.

Shin wae waye itah wannan hanna?????

Shikuma wannan wanda iyayansa suke tunanin aljana ta aureshi wayeshi????             

To be continue

Ur's
     Z33iiyyb3rw3r
BIBIYATA AKEYI         

Bismillahirahmanirrahim

Writing by
                   Zaynab Bawa (z33iiyyb3rw3r)

Page 3
*
            DUBAI

Wani tangameman gida nahango, wanda fadin girmansama tsayawa bata bakine, kyawunsa kuwa kokadan baya misaltuwa domin bansan dawani yare zanmuku bayanin da har zakugane kyau tsaruwar wannan gida ba, hatta tsaron gidan ma, sojojine masu tsaran gidan sunza gayeshi , tako wani sako da lungu gaba da baya,
Azatona tunda kasar larabawa ne nadauka sojajin larabawa zangani amma inah zancen yasha bam bam,

Sojojine kala kala wanda kowace kasa sanda suka bada gudumawa wajen kare lafiyar wannan bawa nasa, kowani soja yana sanyene da kakin kasarsu sojojine bila adadin wanda irga yawansuma bamai yiwuwa bane,

Mamaki da alja'abi suncikani waishin waye wannan dan adam dinda ake gadin rayuwarsa haka. ko sucurities  dasuke gidan shugaban kasa basukai natsaron wannan bawan Allah  yawaba,

MAJOR GENERAL (MG) Abudullahi kukeji daya tamkarda dubu, gwarzon namiji wanda kallonsa kadae ke razana makiyah, ba country dinsa ba kadai
 hatta da sauran kasashen sunaji dashi shiyasa suke bada gudumawa wajen kare lafiyarsa, domin shi mai sadaukarwa al'ummah rai da lafiyarsa ne,

Zaune yake kankujerar tangameman falonsa kafanshi daya akan daya ya jingina da kujera  karkada kafansa yakeyi ahankali cikin nutsuwah da solon birgewa,

Farineh tass kyakkyawan gaske wanda kana kollonsa dakaga kamanninsa da larabawa dogo neh sambal mai faffadan kirji, gwarzon namiji, subhanallah kyawun wannan bawan Allah, abin ba'acewa komai, saidaai hamdala. idanuwansa farare tass kwayar cikin kuwa bakikirin shape dinsu oval ne masu kyawun gaske, gashin kansa bakine sidik, with his cute pink lips, OMG he's damn cute, i don't even knw how to describe him, he's so muah👄

Rurinda wayarsa tadaukane yasashi bude idoh ahankali cikin nutsuwa daukan wayar yayi tareda karata akunnensa.

Amsa sallama yayi sannan  yayi hade dayin murmushi subhanallah kyawunsa baisake bayyana ba saida both side na face dinsa suka lotsa (beauty point)
Abin al'jabin baizoba sanda yafara magana da hausa wadda hakan ba karamin abin mamaki bane
Amsawa yayi da toh abba ammafa akwae abinda nakeyi wadda haryanxu bankarasaba yana maganane cikin natsuwa abba ba halin tafowane cewarsa dadahali danazo cikin week dinnan saboda nima nayi kewarka ina bukatar ganinka to
Call u later baejira mai za'aceba kit yakashe wayan

Wata nauyayyar ajiyar zuciya yasauke kokadan bayason abinda zaisa yaje gida yanxu

Danbaxai iya jira lokaci yacika kafin ya cika kudurinsaba yafi masa sauki yajira lokacin kafin yashiga kasarsa tahaihuwa

Karar saukowar takalmintane yakatse masa tunanin dayakeyi
Wata farar matace wacce bazatafi shekaru hamsin da biyar ba kana kallonta ko tantama bbu dakasan itace mahaifiyar MG Abudullahi balarabiyace
Kyakkyawar gaske
Ko banfada ba kunsan yanayin yanda kyawun larabawan Dubai yake
Karasowa tayi dauke da murmushin dake kara fitoda kamanninsu da MG Abudullahi zama tayi kusa dashi tadafa shi sannan tafara magana cikin harshen larabci

Meyake dmunka haka naga gabaki daya yanayinka yachanja lokuta da dama nakan fada maka kacire wata fargaba bbu wata wacce xatasamu miji kamarka tace bataso kanada kyau da mulki da kuma dukiya bbu wata mahalukiayar da zata kika

Shiru yayi nayan wasu dakika sannan yace ummee bana so asoni dankyawu na ko kudi kowani mulki danake tattare dashi

Mutane dayawa bawae sunasona bane wasu tsoro nane yakesawa sununamin so wasu kuma dan dukiya da mulki yasa suke sona bawai har zuciyah ba wani zafaffen huci yafitar yakara damke hannun ummi dayake rike dashi ummee tajawoshi jikinta ahankali tafara shafa kansa batareda tace komaiba

Aranta kuma tanace Allah kasaukakawa wannan bawa naka wannan jarabawar da ya tsinci kanshi aciki tana tausayin danta ace yakamu dasan wanda basumasan ko tana existing ba

================

Yauma kamar kullum shiri tayi tsab nazuwa makaranta doguwar rigane ajikinta ta yane kanta da gyalen rigar wadda hakan yafito da sihirtaccen kyawunta wanda ba lokaci daya kake kollonta kagano wannan kyawunba

Jakarta ta zara direct dakin babansu tanufa dasallama tashiga sanda ya amsa sannan tashiga tagaisheshi ya amsa da fara'arsa kinfuto kenen eh baba yanxu zanwuce dari biyar yaciro yabata godiya tayi masa sannan tatashi yafibata dakyakkyawar addu'a wadda yakamata duk wani mahaifi yayiwa diyarsa lokacin da zataje wani waje nadaban

Fitowa tayi zuwa bakin titi domin samun abun dazatahau tawuce makaranta duk da chanja mata dasukayi hakan baihanata fahimtar suwaye acikin motar ba adaidata tayi saurin tsara tahau batayi mamakin binta da motar takeyiba har zuwa makaranta sannan ta sallami mai adaidata tayi cikin school din

Sanda suka shiga lectures 80:30 tayi basu suka fitaba basai 11:30 dayake 3hour lectures ne sunafita taji wani irin........

To be continue

Ur's
     Z33iiyyb3rw3r

BIBIYATA AKEYI         

Bismillahirahmanirrahim

Writing by
          Zaynab Bawa (z33iiyyb3rw3r )



Page 4
*
Suna Fita daga lecture taji wani irin yunwa takamata, wanda bazata iya jira bah harsai tanemi wani abu tasa acikinta,
bawani kudin kirki bane a hannunta yasa kawae tashiga wani dan shop a skull din tasaya malt da biscuit

Juyowar dazatayi gam tayi karo da mutum,
baya tayi zata fadi
Cikin tsafinnama dakuma jarumta,yayi
saurin tarota ,yadaidaita mata tsayuwa, dagowa tayi da niyyar kollon ko waye wannan fuskarta cike damasifa,
lokacin daya kuma ida nuwansu yasauka cikinna juna, wani irin faduwar gabane taziyarci zuwa tanufa,
Zubawa junansu ido sukayi na yan dakiku,
Wani irin shock ne yafara bin tundaga kafarsu zuwa kokon kansu gabaki daya wani yanayi suka tsinci kansu mai wuyar fassarawa,

Saurin dauke kwayar idonta tayi daga cikinnasa, dakyar ya tattaro nutsuwarsa waje daya, sannan kwakwalwarsa ta iya tattaro masa kalma daya yace SORRY, yayinda yakafeta da ido, awani irin salon murya irin na mayaudaran mazannan yayi wannan magana,
Wanda idan sunyi sukan sace zuciyar mace, koya takai dajin kanta,
Amma anashi wajan bawae yayi dan yaudaraba saidan besan lokacin yayi wannan salon ba ,
Aikuwa hakanne tafaru da ita domin wannan murya tagama tafiya da imaninta gabaki daya gabanta ne yahau bugawa  dasauri da sauri, cikin dakewa tace is ok tawuce batareda ta kara waiwayowa ta kalleshiba,
bawae kuma dan batasan sake kallonsa ba,
Saidan bataso yamata wannan kallo mai kashe mata jiki.

Matsallaci tawuce Kaitsaye,
dan tasamu tasa wani abu acikinta donko karywa batayiba amma takasa,
abu kamar wasa yanason zama gaske, tunanin wannan bawan Allah yahanata sake,
Zuruf tamike, bata wuce ko inaba sai bakin titi tanemi abin hawa,
Domin yafi mata tawuce gida, bazata iya jure  irin wannann sabon yanayi datacinci kanta, acikinta.

================

Wacece ita abinda yake tambayan kansa kenan dukda dai yayi soyayya da mata daban daban amma wannan yanayi daban yake, komade Wacece ita saina samota yafada afili,
wannan itace tadace dani dama inason nace maikyau da tarbiya wannan ko yanayinta yanuna daga gidan tarbiya take,
Numfashi mai zafi ya furzar sannan ya cigaba da driving cikin kwanciyar hankali da nishadi   waka yasa yana mamin  sayya shafa gashin kansa cikin kwaciyar hankali, yadan daki sitiyari yana kada kai, kana kallonsa kasan akwai nishadi atattare dashi.

================

Mai adaidaita dan Allah juya kamaidani GRA
 federal lowcost mukayi zankaiikifa eh nafasa kajuya nace
Kaitsaye GRA suka nufa yasauketa tabiyashi yajuya abinsa,
wani dan madaidaicin gida nagani mai kyan gaske nan tanufa cikin nutsuwa takwankwasa gate din gidan wani dan dattijoneh ya budeh washe baki yayi cikin fara'a yar baba dama kinanan inanan baba ina wuni lpy klau yar baba yakaratu Alhmdllhy tace atakaice tareda wucewa cikin Kaitsaye wata kofa tanufa
Bude kofan kenan amal tajuyo Ai aguje tazo ayoyo ummah(yawanci akan kira kanwar uwa da umma ) anty anty anty aibashiri anty tafuto Lafiya amal irin wannan kira
Tsayawa tayi turuss sakamakon ganin *hanna* anty yayar hannace uwa daya uba daya tanada aure da yara biyu amal da bashir, *hanna* takanyi wata uku bata leka gidan sister dinta ba saboda Allah yayita mai maqon uwa nan dacan taje sai tafara cewar mamanta shiyasa batacika futaba yanxu haka, halinda ake ciki yau *hanna* watanta biyu rabonta da gidan antynta kunga kuwa hanna mai laipy ceh sosai.

Saurin sauke amal tayi
Kama kunnunwanta tayi da hanna yenta biyu alamunna tuba nake,
Folding hanneyanta tayi irin banhakuraba rausayarda kanta tayi tace pleassssssse ok amma da sharadi ehem inaji karkira yin sati baki zoba nayadda tace cikin sauri karasowa tayi suka rungume junansu jin amal sukayi tanacewa nibanda ni jawota *hanna* tayi suka hada suka rungume

Yawwa ainaji dadin zuwanki dama aiki yamin yawa narasa yadda zanyi yanxu saiki canja kaya mushiga kicin,
Gaskiya anty ninagaji kiyi kayanki kawae, yawwa waeni meya hana baby amal zuwa makaranta,
Kedai bari wae uncle dinsune yadawo daga karatu shine wae yau saidai abatta daizo ganinsu, aikuwa yanxu kusan 12:00 harmafa dataje tadawo

Wallahi abbansu amal dinnanma
Agaisheshi dan kaninsa zaizo sai ahanata zuwa maaranta yajira ran weekend mana kafinya gansu mtsww taja guntun tsaki,
Aibaki saniba duk abinda yarannan yafada yazaune
Nibari wannan bamai karewa bane tashi kidauramin abinci.

Tashi tayi cikin azama tafara girkawa dama ita ba bayaba wajen iya girki bawani abinci mai yawa tayiba dan ita aganinta yin abinci kala kala masuci kalilan almubazzarancine.

Fried rice tayii mai raida lpy wadda tasha kayan lambu kala da iri dakuma hanta wanda akayankata kananu sannan tahada coslow wadda yasha dafaffen koyi bama kamar zeyi magana., zobo tahada wadda yasha kayan kamshi sannan tayi kunun aya tahada ayan da dabino da kwakwa ta markada,
daidai cikinsu tayi wadda babu barna aciki, jan nama tasoya tazuba akan abincin tarufe zuwa 1:30 tagama komai tajereshi adaining ta kimtsa ko ina ta wanke kwanukan da akayi amfani dasu,

Fitowa tayi tagyra ko ina nagidan sannan ta jona burner tazuba turare mai dadin kamshi kamkace meh gidan gabaki daya yadauki kamshi mai sanyin dadi.

Wanka tashiga adakin amal daganan tadauro alwola tayi sallah ta idar lokacin anty harta gama shiryasu amal da bashir itama tayi wanka tashirya,

Fita tayi zuwa dakin anty kibani kaya nasa bude wadrop kidauka mana to Ai naga duk kintaba sawane kajimin yarinya wanda bantaba sawaba kikeso nabaki hava anty yanxu ya mahmood yaga kaya ajikinki nima kuma yagani ajikina haba Ai abunda kunya uhm kyaji dashi bude akwati kidauka to anty tank u

Simple makeup tayi dama ita bama'abociya san kwalliya barkatai bane,
Jan swiss less tadauko dinkin riga da siket tasa,
Ya matukar amsar kalan fatarta, dayake farace amma batacika haske sosae ba saidai kuma baza'a kirata da baka ko chacolate ba,
Tayi mamakin yanda kayan yazauna mata chif chif kaman angwada,
Anty kuma tadan Fita kiba kadan.

Fotowa tayi daga dakin tanacewa anty amma kayannan bama kanki kika dinkawa bako????
Fitowa tayi daga dakinsu amal tana rikeda rigar bashir ahannu, wanda tacire masa ranan kewa,
Au dama wannan kika dauka Toh kinyiwa kanki dama dinkin sallah namiki kuma bazan sakeba, hava anty nidin kinefa,
Eh kedin tawa😏, kantarufe baki sukaji karan door bell, jeki duba barin futoda Su amal, juyawa anty tayi ciki itakuma danufi kofa bude kofan tayi tajuya tanayiwa anty magana, alamu taji kaman Ana kallonta, Juyowar dazatayi daga mutum abakin kofa yakafeta da idoh yajingina ajikin kofa tareda harde hanneyanta,

Baki tabude tana kollonsa jitayi yace......

To be continue

Ur's
      Z33yyb3rw3r

BIBIYATA AKEYI         

Bismillahirahmanirrahim

Writing by
            Zaynab Bawa (z33iiyyb3rw3r)

Page 5

*
Baki tasake tana kallonsa jitayi yace
Rufe bakin,
Saurin rufe bakin tayi sannan takauda kai gefe,
Tareda jan dan siririn tsaki ahankali tafara magana damme dakabugeni a school,
Kuma kabini abaya haryanda nazo kuma kasake bibiyata
Tsaki takara ja
Gani tayi yazuba mata idoh kaman wani wanda yakeson gano wani abu atattare da itah, kara tamke rai tayi cikin tsafin murya tace mekuma kake kallo,
Wani abu nakeson ganowa shin wae kece kuwa ta dazun nan kallon gefe da gefenta yayi wadda hakan yasata itama bin yadda ya kalla da kallo

Kai bake bace,
 rike havansa yayi cikin zolaya yace oh namanta ashe yanxu kinyi makeup ne wani kololon bakin cikine yatokareta,
Wato nufinsa dazu batayi kyau ba kome,
Gyaran murya yayi tareda cewa idan kagama shirmenka saikaban hanya nawuce,
Sosa kyeyansa yahauyi, yayah bafah shirme nakayi ba koma meye nidai bani hanya *hanna* wanda kunya tabi tacikata jin kiran mijin anty da yaya Wato shine kaninnasa Wato ba ita yabiyo ba oh sh*t tace tareda dan dukan goshinta da tafin hannunta, meyasa na aikata haka wayyo yanxu shikenan zaidauka tunaninsa nakeyi tafada acikin ranta,

Saurin juyawa tayi tashige daki, murmushi yayi sannan yafurta,
She's amazing, ahankali yadda yah mahmood bazaijiyoshiba, abinda bai saniba shine tun tsayuwarsu yake kare musu kallo tass, daya Bayan daya. idankagama saikawuce mushiga cewar yah mahmood, Sosa kansa yayi sannan yashiga da sallama, antyne tafuto cikin fara'a tanamasa barka, yaude naga najeeb, dariya yayi sannan yadan waiga ko zaiga ta inda zata bullo amma shiru, yaya mahmood dake zaune gefensa yagane wanda yake nema dafashi yayi cikin sauri yajuyo daga masa gira yayi, mekake nema, bbu kawae inaduba yanayin gidanne ow kawae ya mahmood yace danyaga rainin hankalin najeeb yawuce yanda yake tsammani,

    Waye najeeb??????
            NAJEEB
najeeb kanin mijin antyne wanda yakasance shine autansu,
Su bakwae ne awajan mahaifinsu , iyayensu asalin yan bauchi ne wanda yanxu hakama anan suke zama babansu yarike mukamai da yawa a high court,
Sanda yakai matsayin Grand cady sannan yayi ritaya, matarshi tafarko itace hadiza, hadiza irin mutanan ne masu masifa,
Amma kuma tanada kirki sosai dasanin darajar dan adam, yaranta hudu da alhaji masa'ud babbar yarsu itace ikilma wanda yanxu tanada aure da yara shida sai aminu wanda shima yaransa hudu dakuma halima wacce ke aure acikin garin bauchi da yara shida itama, awajan haihuwar salima ne Allah yamata rasuwa, tarasu tabar yarta kyakkyawa maikama da ita, alhaji mas'ud yayi kuka narashin, mata mai nagarta, daga baya yafawwalawa Allah komai, yarungumi yayansa hudu databari hannu bibiyu, yaki jinin kallonsu cikin bacin rai,

Ana haka Allah yakawo wani wani justice, daga maiduguri, asalunsu shuwane dayarnsa mata da maza, lura yayida alhaji mas'ud baitaba Gani yayi maganar matarsa ba, adah yayi tunani koh danbasu saba sosai bane Amma yanxu abin yasha bambam dan wata rana yakirashi akan yazo gida yasameshi dan akwae wasu takardunda yakeso yazo yakarba yaje office yayi aiki akansu, sanda yakara kusan, hour biyu akan yadda ya umurceshi yazo, Bayan ya isoneh yake tambayrsa mayya zaunar dashi nan yake shaida masa cewa yatsaya shirya yaransane tambayarsa yayi ina matarsa nan yake shaida masa Ai Allah yamata rasuwa, hakuri yabashi sannan yace masa zama bbu mata banasa bane, yanemi wata ya aura domin yaransa, shaida masa yayi yanatsoron ya auro wanda zata musgunawa marayun yayansa neh shiyasa don yanxu samin mata tagari yayi karanci.

Shiru justice yayi wani tunani sannan yayi gyaran murya yace, to Ai bakazauna hakaba, gayata nan nabaka dan inada tabbacin baxata musgunawa yarankaba, amma kaje kayi tunani kafin kayanke hukunci, shiru yayi sannan yamasa godiya yatafi,
Bayan kwana biyu ya yanke hukuncin amincewa da auran, amma kuma akwae fargaba aransa don baisan wani irinzama dasuyiba Bayan haka gata dangin shuwa kuma masuji da dukiya da mulki amma kuma bazai iya duban fuskan justice yace bayason auran yarsaba, zuwa yayi yashaida masa ya amince, wanda tuntuni ita ba'asamu matsala tawajan tava danta kasance mai biyayya ga iyayenta, dangin mahaifiyarta ne suka fara magana akan za'adauki karamar yarinya akaita bauta wajan yara, dan wannan auren bautane, toshe kunnuwanta tayi dan ita tansan mijinta kuma tana respecting duk wani wish nasa. cikin kwanciyar hankali yaturo magabatansa akayanke rana wanda suma danginsa bakarin farin ciki sukayiba ganin shidakansa yace sujemasa tambaya, dansunyi akan yayi aure harsun gaji, andaura aure ba'ayi wani shagaliba walima kawae akayi akakai tadakinta, dafarko yayi zaton samun matsala daga wajanta amma hakan bata faruba dan tana kula da yaransa kamar ita ta haifesu, dalilin dayasa yadauko salima daga gun mahaifiyarsa kenan yadamka mata

ba'a dade dayin aurenba ciki ya bullo tahaifi yarta fara sol mekamada mahaifinta amma hasken mamanta, itada kanta tabukaci asawa yarta hadiza bakaramin dadi yajiba, Bayan tayaye halima wacce suke kira da maamaa ta haifi danta mahmood shima kammannin babansa sak sanda tadau shekaru kafinnan ta haifi najeeb wanda shikuma bbu abinda yabaro namahaifiyarsu sai ma ince yaso yafita kyau, ammashi kalan babansa yadauko dan bakine shi daganan bata sake haihuwa ba nan duk gidan suka daukiso suka daurawa najeeb tundaga kan iyayen har yayun bawanda yakeson laipyn autansu,

Najeeb dan kimanin shekaru ashirin da shida kykyawane baki yanada tsayi amma ba sosaiba yayi karatunshi tundaga secoundry har zuwa doctarin deegree dinshi akasar waje wanda yanxu dawowarsa kenan daga can kasar yayi gam da katar da zinariyarshi😍😍

      Back to labari         tashi anty tayi tanufii dining sannan tamusu Iso karasawa sukayi dukkansu kowa yakama kujera yazauna kwala mata kira anty tayi kan tafuto itada amal suci abinci sannan tadauko wa uncle dinsu yaganshi,

Futowa tayi daukeda bashir akafadanta sannan dayan hannun yana rikeda amal zuba mata idanuwa yayi tundaga nesa yakasa daukewa jiyayi an dafashi........

Ur's
      Z33yyb3rw3r

BIBIYATA AKEYI         

Bismillahirahmanirrahim

Writing by
           Zaynab Bawa (z33iiyyb3rw3r)

Page 6

Sorry for the last Page there are some several mistakes wllhy bansamu nagyaraba.

*
Jiyayi andafashi saurin juyowa yayi, nan take kuma kunya ta lullubeshi, ya mahmood ya kamashi yana tsare masa kanwar mata da idoh,

Karasowa tayi tajama amal kujera tazauna sannan itama tazauna, dama kujeran dining din mai kujeru shidane, anty nazaune kusada yah mahood, najeeb kuma yana dayan gefen ya mahmood itakuma tasa amal atsakiyanta da najeeb,

Anty tatashi tafara saving dinsu tana bude food flask din wani kamshi yadaki hancinsu lumshe ido najeeb yayi sannan yabudesu, saukesu yayi akan *hanna* wadda ita batasanma yanayiba, dan tunda ta iso tadauke idanta daga kansa,
Anty ne data zubawa amal abinci saurin rike hannun anty anty tayi, owh owh nibake dakiyi saving dinaba ni ummah ne data zubamin, ohoh kyaji dashi keda ummankin,

Juyawa tayi wajan najeeb daniyar zuba masa saurin langabar da kansa gefe yayi sannan yace owh owh nibake daki zubamin ba ummane data zubamin yakwaikwayi maganan amal amma kuma harcikin ransa yafiso tazuba masa, wata harara tawatsa masa kamar idanunta dasu fadi kasa, idoh daya ya kanne mata tare dayin murmushin dashikadae yasan ma'anarsa,

Juyawa anty tayi ta kalleta, maza tashi kizuba muku abinci, batareda tayi wani tunani ba dan Azatonta koh yabi maganar amal ne kawae, shikuwa yaya mahmood yagama gane yanda yadosa,
Idan haka tafaru bakaramin farinciki zaiyiba dan yafi kowa yawa kaninsa addu'ar samun mace tagaari, fatanshi kawae Allah yasa bata tsayarda miji ba,

Kunkuni tatashi tanayi ciki ciki tamikawa anty bashir, no kawoshi haka nan muryar najeeb takatseta, yitayi kamar bataji shiba takara mikawa anty yaron wae bakiji mai akafada miki bane, kibashi yaron turo baki tayi, sannan tanufeshi ta dangwara masa yaron, akan cinyarsa, anty baki kawae tasake tana kallon ikon Allah,
Idan kingama shirmenda kikeyi saiki zuba muku abinci, kara turo dan bakinta tayi,
Wani irin kyau yaga tamasa tashi daya tsikar jikinsa tazuba, gashinda ke kwance ahannayensa suka tashi, Jiyayi kaman yaje yayi kissing din bakinta dan yanda take turoshi bakaramin kyau tayiba, saida shi Allah yayishi bameson taba matar daba muharramarsa bace, with time yafada acikin ransa dan duk randa Allah ya mallaka masa ita amatsayin mata wannan dan karamin bakinnata daga ranan bazai kara yin tsauri mawaniva,

Zuba masa abincinda tafarayi ne yadawo dashi daga tunanin daya wulla, zuba masa tagamayi sannan takoma kan amal itama tazuba nata tazauna,

===============

Inah mukabar masu *bibiyan* *hanna* ne tun fitarta daga gida suka fara binta har tashiga lectures tafito, fitarta daga lecture zuwa shop duk lokacin suna bib *bibiyarta* Bayan takarasa shop ne daya daga cikinsu fitsari ya mugun kamashi, dama kunsan ance tsautsayi baya wuce ranarsa domin oppotunity come at onces just like mistake come at onces either dakadauki tsaawon shekaru kana kare abu but na lokaci guda kayi sake da wannan kariyar wannan mistake din da za'asamu ayan secound itx really hard to make it up,

Fitsarine sosai yarikeshi wanda bazai iya jiraba gawajen wajen wucewar jama'a balle yayi awajan, yabukaci dayan dayakai shi yayi aiba wata damuwa tunda akwae mutane ashop tun har dasu dawo kafin asallameta,

Rakashi yayi kafin sudawo abinda suke gudu ya auku wandasu basuda masaniya akan faruwar hakanma domin alokacin najeeb yabige hanna haryaji zuciyarsa takamu da sanda, itama hakanne tafaru awajanta luv at first side,

Dawowarsu yayi daidai da fitowarta daga shop din, nan sukaci gaba da binta, wanda saken dasukayi nayan wannan minute din yana daidai darasa rayuwarsu,

Harzuwa lokacin da  tajuya me keke napep zuwa gidan antynta harnan suna biye da ita sanda tazo gidanne ta shiga sukuma sukayi parking car dinsu, sunajiran fitanta,

Koda lokacin da najeeb yashigo tareda yaya mahmood yazo wanda yaje hargida yadaukeshi kuma sunriga da sunsan motar yaya mahmood kuma sunsan matsayinsa a wajanta so basu damu daduba motarshi ba koda wani acikinta dake motan nada bakin tinted,

Haka yayita kallon ta harsuka karasa cin abuncin, anty amma kin iya abinci wallahi nima Allah ya bani wacce ta iya girki yafadi haka tareda satan kallanta ta kasan idoh, to Ai baninayi ba cikin zumudi yace wayayi gata Zaune kusa dakai, hmmm yaja gauron numfashi anty amma mijinta yayi sa'a sainaji dama nine wannan mai sa'ar,

Siririn tsaki taja kaifa kafara wuce gona da iri ha'ah ta murguda masa baki, wow😍 gaskiya fushi yana miki kyau kamar karkiyi dariya,hakan dayafada ne yasata murmusawa wow to Ai kuma dariyan yafi miki kyau kainama kasa tantancewa

Ahaka yayita jan ta da kalamai masu dadin sauraro harta bashi phone number dinta,
Saida tayi la'asar kafin tafara shirin tafiya,
Bayanda bayiba akan yasauketa agidah amma fir taki,
Haka sukayi sallama da anty kafin tafuto da niyyar wucewa gida batayi mamakin ganin motarsu,
Sanda tayi dan tafiya kafin tasamu abin hawa gida tawuce,

             DUBAI

Major general MG Abudullahi ne Zaune a office gabaki daya tunda karfe 11:30 tabuga a agogon nigeria wadda yayi daidai da 2:30 a agogon akasar dubai wani irin faduwa gabansa keyi kuma yarasa dalili tunyana daurewa avun har zazzabi yake shirin sa masa ba shiri yabaro office yayi gida amma duk da haka yakasa samun nutsuwa kamar wanda wani mummunan lamari ke shirin faruwa dashi,
Captain ahmad yafada cikin dagun murya cikin tsafin nama wani dan saurayi wanda bazaifi kimanin shekaru 30 ba ya isoh wajen cikin girmamawa yace Gani yallabai yisauri kakiramin Captain bala jiki harayana bari yaciro waya a aljihunsa dan yasan halin ogannasa bayasan wasa barinma daya fahimci ransa yana bace, ringing daya akadauki wZ33iiyyb3rw3rikawa MG wayan yayi ya karba tareda karawa a kunnensa.....

To be continue
         


Ur's
      Z33yyb3rw3r

BIBIYATA AKEYI         

Bismillahirahmanirrahim

Writting by
               Zaynab Bawa (Z33iiyyb3rw3r)

 _This Page is sincrely dedicated to u My dear *Ayeshert* *Aly* *garkuwa* u r such a wonderfull person i want u to know that u r _amazing_ so _much_ _love u_

Page 7

*_

Saurin karban wayan yayi tareda karawa a kunnensa, yafara, magana duk da bawae jin maiyake cewa nayiba amma nafahinci yanayin sa yasauya dan damuwar da take fustarsa ta sassauta, duk da dama bawae yakasance mutum mai fara'a bane amma akan iya gane lokacin dayake cikin bacin rai,

Sauke wayan yayi daga kunnensa tare da sauke wata nauyayyar ajiyan *zuciya*
Bawae dan yagama yadda da abinda Captain bala yace bane, amma hankalinsa yadan kwanta, domin yasamu sassauci daga yanda zuciyar sa ke bugawa,

Mikewa yayi akujerar dayake Zaune, ya lumshe idanuwansa, abubuwa kala kala yake sakawa acikin *zuciyarsa*

================
Bata isah gida ba sai karfe biyar na yamma, tura dan karamin kofar dake jikin gate din gidansu tayi tashiga da sallama duk da tasan bakowane awajan dazai amsaba amma yanada kyau shiga gida da sallama,

Cikin gidan tawuce kaitsaye, tasamu ammah zaune tana yanke, farcen kafanta, sannu da gida ammah tafada koda batasa ran amsawaba, amma dabi'ar tane koh bazata amsaba saita gaishe ta,

 Idontane yakai kan kayan dake jikinta, ke zonan tayi saurin kwala mata kira, yitayi kamar batajiba dan idan zaka shekara kana ce mata ke bazata amsaba,

Sanin halinta ne yasa tayi saurin cewa *hanna* badake nakeyiba juyowa tayi au banji lokacin bane, Wani kululun bakin ciki ne yatokareta, aranta tanacewa yarinya batasan komai ba sai rashin kunya, afili kuma tace A'inah kikasamu wannan kayan jikinki ?????

Kallon gefe da gefenta tayi sannan tadago tace wanne???

ungo naki wannan najikinki mana to aini banga wani kaya ajikina ba nawane, oh namanta ashe ance idan mutum yafara tsufa yanada saurin mantuwa,

Tana fadin haka tayi saurin juyawa, dantasan abinda ta aikata don kokadan ammah batasan tsufa, Saurin shigewa sashin mama tayi tabar Ammah nata surfa ashar,

Shigewa tayi tana dariya afalo tatararda mama Zaune tana kollon wisal hausa, kewani irin shashancine haka zaki shigowa mutane daki babu sallama kamar wata tababbiya, turo vakinta tayi mana nayi sallama  fa bakiji bane, kyaji dashi dai tafada tareda juyawa taci gaba da kallonta,

Wucewa tajeyi mama tayi saurin tareda keh A'inah kikasamu wannan kayan kuma, mama gidan anty na'ilah fah naje, shine kika samata kaya kaimama me shiga tsakanin yaya da kanwa fa zaiji kunya.

Uhm kawae tace tacigaba da kallanta,  Bayan mangaruba kamar yadda suka saba kowa nacikin gida yana Zaune, antadi saikuma yan habaice habaicen daba'a rasasu acikin gidan, itade hankalinta gabaki daya baya wajensu yanakan phone dinta,

Jira takeyi kawae kiran najeeb yashigo, amma shiru saida
Har tayi shirin kwanciya tagama cire rai da kiransa, dan harta kwanta bacci, taji wayanta yafara ringing, koda taga number ne tarigada tasan waye yasa batayi Gigin daukaba sanda ta katse,

Tajira koda'a sake kira amma shiru harataji haushin kanta naja masa aji datatsaya yi gashi yanxu yakikira, Wani irin haushin kanta takeji nakin daukan wayan

Kusan 30 minute yakara kafin yasake kiranta, mai halidai bayafasa halinsa dan sai wayanna dab da tsinkewa kafin tadaga, shiru tayi takiyin magana, sallama yamata daga nasa wajan, amsawa    tayi adakile,

Kingane waye A'a tabashi amsa shiru yayi danransa yadan sosu datace masa A'a kuma yasan bawai bata gane waye bane saitsan tsan rainin wayo,

Shitunda yakema bai taba kiran mace taki dauka ba saiyau, najeeb neh, oh yakake, lafiya ya mama da baba, kowa kalau, yayikyau amma meyasa kikace baki ganeba, hmm tace kawai tana masa magana cikeda rashin sabo,

Haka yayita jan ta dahira mai dadi hartadan sake dashi sai wajen 11:00 sukayi sallama dan bacci ne tab a idonta,

Sanda ya tabbatar da, yadasa mata wata irin soyayyarsa a zuciyarta kafin yabarta, bacci ne mai dadi yadauketa, cike da farin ciki da annashuwa,

Zaune take abakin wani ruwa awani hadadden beach gawasu tsuntsaye masu kyan gaske sunata zagaya wajan najeeb ne Zaune agefenta, inibi yadauka dake cikin wani faranti agaban Su cike yakeh kayan marmari,

Kana kallonsu kasan suna cikin wani irin  yanayi na nishadi, Da farin ciki domin yadda fuskokinsu ke dauke da murmushi mai tsadan gaske,

Dauko inibin yayi yakaimata bakinta, lumshe idoh tayi hadeda bude bakinta, shirun dataji ne yasata bude idoh,

Sojojine zagaye da wajan da suke Zaune ga najeeb ahannun wani mutum wanda kana kallonsa daka tabbatar da balarabe ne sak

Yasawa najeeb bindiga akansa, magana yajuyo yanayi yana kallanta,
 *Hanna* meyasa bayajin magana nahanaki meyasa kikeson sa rayuwar Su cikin halaka,meyasa kikeson saka zuciya na cikin kunci zankasheshi kuma zankashe duk wanda ya kusanceki da sunan so,

Ke tawace nikadai dan nafi kowa sanki, yana gama fadin haka ya sa kan bindigan akahon zuciyar najeeb sannan yadana kunamar bindigan wani irin raza nannan ihu tasake,,,,,,,,,,,,,

To be continue

Ur's
     Z33iiyyb3rw3r

BIBIYATA AKEYI         

Bismillahirahmanirrahim

Writing by
           Zaynab Bawa (z33iiyyb3rw3r)

 _This page is dedicated to _you_ *_hajja_* *_ceh_*

Plx kuyi hakuri wannan page din bayawa

   Page 8

*
Wani irin raza.. Nannen ihu tasake... Tashi daya kuma tafarka daga wannan bacci mai mummunan mafarki

Ihun datayi ne yasa mama saurin farkawa daga bacci
Saurin riketa tayi ita,,,, kuma sai fisge fisge takeyi tana ihu,,,,,,,, na shiga uku sunkasheshi wayyo Allah na dama nasan baxasu bari in aureshi ba wallahi sun kashe shi,,,,,,,, duk maganan datakeyi cikin kuka take yinsa, Addu'a mama taringa tofa mata duk wanda tazo bakinta,,,,,,,,,
     Dan itama gabaki daya tarude,,,,,,,,,,,,.
Sanda tadauki kusan awa biyu awannan yanayin,,,,,,,,, kafin tasamu tadan lafah,,,,,,,,, aranan baccin da batayi ba kenan domin gani take kamar wayannan mutane suna iya dawowa,,

Daga ita har mama babu wanda yarintsa,,,,,,,,,,,,,,,,,
sallah suka kwana sunayi suna rokon Allah,,,,,,,,,, yakaresu daga sharrin makiya,,,,,,,,,, dakuma sharrin mutum da aljan,,,,,,,,,,,,,,,,, 

Koda asuba tayi,,,,,,, tada ikama kawae sukayi suka gabatar da sallan asuba,,,,,,,,,,,, bawanda yayi gigin komawa bacci aciknsu,,,,,,,, azkar sukaci gaba dayi har rana tafuto,,,,,,,,,,, sai lokacin hankalinta yakwanta da dad`a tabbatarwa da mafarki ne ba gaskiya ba,,,,,,,,,,,,,,,,

Bayan gari ya waye ne,,,,,, tashiga dakin babansu da gaidashi,,,,,,,, ganin idanuwanta a kumbure ne yasa shi zaida ita,,,,,,,,,,,,,,,, *hanna* yakira sunanta cikin yanayi nason gano wani abu dake tattare da ita,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,, amsawa tayi sannan yace dawo nan kizauna,,,,,,,,,, zama tayi cikin nutsuwa
        Meya faru haka naga idanuwanki sun kumbura gabaki daya,,,,,,,
      Shiru tayi nayan wasu sakonni,,,,,,, danbata da amsar tambayarsa,,,,,,,,,, shirun datayine yasa shi fara ganewa akwae abinda ke damunta,,,,,,,,,,

 *Hanna*  badake nake magana ba,,,,,,,,,,, babu komai da baba jiya bansamu bacci bane nayi karatun test, kuma gashi yace yadaga zuwa next week,

Tafadi hakanne domin kare kanta,, daga tambayoyi,,,,,,, kuma tasan tabbas idan yaga batayi shirin tafiya makaranta ba sayya tuhumeta,,,,,,,,,, kuma yau ayanda take batajin zata iya zuwa, makaranta,,,,,,,, toh adai ringa hutawa Dan irin haka karatun sayya ki zama koh ,,,,,,,,,,,,

Toh kawae tace sannan ta tashi tafuta daki tawuce,,,,,,, takwanta,,,,
Tayi tsurfi cikin tunani batasan mama tadade akanta tana kallon taba,,,,,,,,,,,,,,,,,

Taba ta tayi cikin firgici ta tashi tazauna,,,,,,,,,,,, gefe mama tasamu ta zauna itama,,,,,,,,,, *Hanna*  inason intambayeki kuma banason kimin karya koki boyemin wani abu daga cikin abinda kika sani,,,,,,,,,,,,,,,,
     Dan na gaji da kallon ki kullum cikin damuwa na dade dasanin akwae abinda yake damunki kina boyemin,,,,,,, amma nayi miki Shiru toyau gaskiya nakeson kifada mun,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,

Meyake damunkii????? Wannan dakike mafarki an kasheshi wayeshi????? Kuma waye kike ambada kan dama kinsan bazai barshiba????? Ajere da zuba mata wannan tambayoyin

Shiru tayi na yan wasu dakikae kafin tafara bawa mama labarin tun lokacin da tasamu Ammah da kawarta suna tadi zuwa jiya haduwar su da najeeeb,,,,,,,,,,,,,,,

Abu daya taboye mata shine wayannan mutane dasuke bibiyar ta Dan,,,,,, idan tafadawa mama batasan wani irin hali zata shiga ba,,,,,,,,,,,,,,,,

Yanxu ma kenan kuka takeyi hadda shassheka,,,,,, balle taji labarin wannan mutanen damuwa saita yi mata yawa,,,,,,,,,,,,,,,,,

Kuka takeyi tana meyasa,,,,,,,,, Hanna meyasa baki fadamun tunda wuri ba wannan ba karamar matsala bace,,,,,,,,,,,,, dole mudage da Addu'a kar Allah yabasu galaba akanmu,,,,,,,,,,,,,,,, bansan me muka tare musu ba wallahi ta Allah batasu ba kuma in sha Allahu saikin auri mijinda zai soki ya kaunaceki idanma sunaso babanku yagaji Z33yyb3rw3ri wanda zai wulakantaki ne to ta Allah batasu ba kuma wallahi damu tsuba nidasu,,,,,,,,,,,,, sai na yakesu da kafin Addu'a,,,,,,,,,,,,,

Share hawayenta tayi,,,,,,,,,,,,,, sannan tacewa *Hanna*  da Allah share hawayenki wallahi Allah baxan bari suci galababa tana gama fadin haka tatashi tafuce,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,, wani Kuka ne mai karfi ya kara kubuce mata ci gaba tayi da rerashi kaman wanda dama an aikota duniya Dan kukane kawae,,,,,,,,,,,,,,,

Sallamar wanda tajine yasata saurin hadiye kukanta tareda,,,,,,,,,,,,,,

To be continue

Ur's
      z33iiyyb3rw3r
BIBIYATA AKEYI         

Bismillahirahmanirrahim

Writing by
            Zaynab Bawa (z33iiyyb3rw3r)



Page 9

*
Sallamar Wanda tajine yasata saurin hadiye kukanta,,,,,,,,  saurin
 goge hawayanta tayi,,,,,,,,,,,,,, damin bataso afahimci akwae damuwa atattare da ita,,,,,,

Fita tayi daga dakin aguje taje tayi hugging dinta,,,,,,,,,, duk wani damuwa dake tattare da ita jitayi kaman ba wani damuwa bane,,,,,,,,,,, Don Baza ta iyah misalta irin farincikin da take cikiba,,,,,,,,,,,,,,,, bawae Kuma Dan Bata cikin damuwar ba,,,,,,,,,,,,,,,,, saidan farincikin ya danne damuwar da take ciki,,,,,,,,, ,,   

Juyowa tayi itama cikin farin ciki takara hugging dinta,,,,,,,,,,,,,,,,, Koda ba'a fada bah kallo daya zakayi musu ka gwano farin cikin dake tattare dasu,,,,,,,,,,,,,

Gyaran muryan baba ne yadawo dasu cikin hankulansu,,,,,,,,,,,,
To yaran mama sun hadu Sai wani farinciki da annashuwa kukeyi koh daga zuwanki Kinga yar uwarki,,,,,,,, koh azo agaishe da baba gashi Yana shirin Fita office,,,,,,   mama ce ta amshe maganan da cewa au danma bakaji meh jiya tacemun ba,,,,,,,,,,,,
Wai meshiga tsakanin Yaya da kanwa zaiji Kunya,,,,,,,,, Dariya duka suka saka daga baban Har anty hajja da zuwanta kenan,,,,,,,,,,,,,,,,, toh nidai nafita sai nadawo tukunna ma gaisa cewar baba sannan yasakai yafice,,,,,,,,,,,,

Daki suka nufa dukansu,,,,,,,,,,,,,, sai farin ciki sukeyi
Sai da suka shiga ne mama tarufe ta da fada,,,,,,,, kancewa menene dalilinta nakin fada musu tana hanya aiko ba komai ma tayaki da addu'a wannan tafiya Bata wasa ba ga Yara aiko abincii matana dar Miki,,,,,,,,,,,,, mama aitoh bebaci bah tunda Ga wannan beb din kawae tashiga kitchen tadafa mana,,,,,,,,,,,,,,,,,

Cikin farin ciki *Hanna*  tatashi da niyar zuwa ta daura musu abinci ,,,,,,,,,,,,,, kitchen da nufa tafara girka musu abinci cikin dan kankanin lokaci,,,,,,,,,,,,,, tagama hada musu breakfast,,,,,,,,, domin itama bawae tayi Karin kumallon bane,,,,,,,,,,,

Gama kimtsa komai tayi sannan takai musu falo ta ajiye musu komai,,,,,,,,,,,,,
Sannan tadawo tazauna,,,,,,,,,,, jawo yarinyar anty hajja tayi tazaunar da ita bisa Kan cinyarta,,,,,,,, duk da bawani sabawa sukayi da yaran anty hajja sosai ba sakamokon nisan wurin rayuwa dasukee,,,,,,,,, Amma tasan dasu ebe Mata wata kyawar,,,,,,,,,,,, Dan anty hajja takan Dan dade kafin takoma,,,,,,,,

Zama sukayi sukaci abinci sukayi nakk Kamar babu wata damuwa atattare da dasu,,,,,,,,,,,,,,,
Sai Bayan sungamacin abinci ne anti take tambayan cewa koh suna tattare dawata damuwa née?????   Mama ne tafara Bata labarin abinda yake faruwa Dan kokadan bataji zata iya boyewa yarta damuwar taba,,,,,,,,,,,,,,,,

Tashi *hanna* tayi tashige Daki tabar mama tana Bawa Yaya hajja labarin,,,,,,,,,,,,,,

Wajan wayarta tanufa dake Kan bed side drawer,,,,,,,,,,,,,,,
Daukan Wayan tayi missed calls tagani bbu adadi wadda duk yawancinsu na Amira neh  sai 3 miss calls na najeeb,,,,,,,

Zama tayi agefen Gadon tana tunani shin Kota kirashi ne kokuma tafasa,,,,,,,, Bata Gama yanke shawara ba,,,,,,,,,,,  taji muryan antyy tana kwala Mata Kira,,,,,,,,,,,,

Tashi tayi cikin nutsuwa ta nufi falo,,,,,,,,,, wurin anty tanufa tazauna,,,,,,,,,,, hanunta anty tarike sannan tafara magana  cikin murya medauke da tashin hankali acikinta,,,,,,,,,,

 *Hanna* meyasa Daki boye mana wannan lamari kinsan wannan ba karamar matsala bane,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,
Shin kina yawan mafarki na tsoro ne *Hanna* da kanta ke sunkuye tana wasa ta yatsun hannunta ta girgiza Mata Kai,,,,,,,,,,,,,,,, toh kokuma kina mafarkin kin haihu Kara girgiza Kai *hanna* tayi,,,,,,,,,,,,, baki taba mafarkin ana saduwa dake ba,,,,,, anty takara ce Mata jefo Mata wata tambayar,,,,,,,,,,,,, cikin  Jin kunya takara girgixa Kai,,,,,,,,, kifadamana gaskiya domin samun mafita dagowa tayi,,,,,,,, ta kalli anty sannan tace Allah duk abinda nafada gaskiya ne,,,,,,,,,,,,,,,,,,,

Shiru mama da anty sukayi Dan sunkasa fahimtar yadda wannan lamari ya dosa,,,,,,,,,,,,,,,,,,

Anty ne tayi karfin halin cewa wannan lamari da daure Kai yake,,,,,,,,,,,,,,, Amma bbu abinda yafi karfin Allah muci gaba da Addu'a in Sha Allah zamuci wannan jarabawar danna tabba ta wannan jarab tace da ubangiji,,,,,,,,,,, Kuma in Sha Allah damu cinye wannan jarabawar

Numfashi mama tasauke sannan tace in Sha Allah da Allah muka dogara kuma damu dage daga neman tsari daga wajansa,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,

Rurin da wayar Hanna tadauka ne yasasu saurin juyawa suna kallon ta shiru tayi Kamar baxata dauka ba Dan warning din da aka Mata cikin mafarki Har yanxu Yana yawo akwakwal warta,,,,,,,,,,,,,,,,

Kallon ta anty tayi tamata alamu da idoh kancewa ta amsa wayar,,,,,,,,,,,,,,,, amsawa tayi hadeda karawa akunnen ta,,,,,,,,,,,,

To be continued

Ur's z33iiyyb3rw3r

BIBIYATA AKEYI         

Bismillahirahmanirrahim

Writting by
             Zaynab Bawa (z33iiyyb3rw3r)

My first novel

Page 10

*
Alamu anty tamata da idoh Akan tadauki wayar,,,,,,,,,,,,,,,,,,
Dauka tayi hadeda karawa akunnenta,,,,,,,,
Sansanyar muryarsa ne tadaki dodon kunnenta,,,,,,,,,,,, sanda ta lumshe idoh Dan wani sanyi ne yaratsa zuciyarta jitayi kaman Wanda tashekara bataji muryan saba,,,,,,,,,,,,,,,,,,
Wani irin sonsa ne yakara shiga zuciyarta,,,,,,,,,,,
Jitakeyi Idan aka rabasu kaman ana shirin rabata da rayuwar ta NE,,,,,, ,,,,,,,,,,, Dan haka takeji
Bazata taba Bari ayi nasara akansu ba
Hello,,,,,, Hello,,,,,,, saida yayi sau biyu kafin yadaawo da ita daga tunanin data Lula,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,

Kallon anty hajja tayi sannan takalli mama,,,,,,,,,,,,,,,,,, duk sun zuba Mata idoh jira sukeyi suji mai za ta fada,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,da gudu tatashi tashige daki tana kyalkyale Dariyah ,,,,,,,,,,,, tana shiga daki tayi saurin Kara wayar akunnenta Dan azatonta ma wayar ta yankeh,,,,,,,,,,,,,,,,, sallama tayi ajiyar zuciya yasauke,,,,,,, sweety namiki laipy ne nayi ta Kiran wayanki baki daukaba kuma yanxu nakira kinki magana,,,,,,,,,,,,,,,,,,, wani dadi ne ya maimayeta Sai hamdala take yiwah ubangiji,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,, dama akwae ranan da Allah zai nuna Mata randa za'akirata da suna mai dadi haka,,,,,,,,,,,,,, domin itah harta cire rai amma dayake ba'acire rai da rahamar Allah Sai gashi yamata zabi nagari,,,,,,,,,,,,,,

Masu karatu kada kuyi zaton waiko *hanna* tadade bbu aure ne,,,,  ah ah,,, Dan kwata kwata Baza tafi shekaru Sha Tara bah,,,,,,,,,,,, Amma ku kiyasta yanda mace dataji ace tuntasowar ta ace bbu Wanda yataba zuwa wajanta da Susan Yana santa,,,,,,,,,,,,,,

Abinda mugun mamaki duk munin mace bata rasa masoyi,,,,,,,,,,,,, ballanta ita *hanna* datana da kyawunta    dole abin zaida meta daga itah Har mahaifanta kuwa,,,,,,,,,,

Kara katseta yayi sweety bakya ji nana,,,,,,,, um inaji mah,,,,,, huh,,,,, shine kika kyaleni,,,,,,, sorry toh,,,,, OK yawuce amma meyasa dazu kika ki daukan kiran,,,,,,,,, farko nadau kina school kuma naje wata Amira Wai tace ita friend dinki ne tashaida min baki zoba so shine hankali na ya tashi,,,,,,,,,,,, hope komai   lafiya,,,,,,,, lafiya klau kawae Dai anty ne tazo ninama manta da phone Dina,,,,,,,,,, haba shiyasa naji gabaki daya kina cikin farin ciki,,,,,,,,,,,
Toh yanzu kawae ni danzo anjima kibani address,,,,,,,,,,, lahhh rufamin asiri Dan Allah,,,,,,,,,,,,,,,,, batarai yayi kaman Wanda take ganinsa,,,,,,,,, dalilin ba kyasona shiyasa bakiso nazo yanda kike koh?????   Marai raice murya tayi,,,,,,,,, No bafa haka nake nufi ba,,,,,,,,,,, to me kike nufi in ba haka bah,,,,,,,,,,  Allah baban mu zaiyi fada,,,, me yasa zaiyi fada toh??????  Aishi se'an tambayeshi kafin afara zuwa hira wajen yarsa,,,,,,, mehakan yake nufi kenan,,,,,,,, cikin fargaba da zullumin abinda zaije yazo Dan batasan ya zai dauki lamarin ba,,,,,,, Ina nufin saida izininsa ake hira da yarsa,,,,,,,,,,,, wani dadi ne yamaimaye masa rai donko ba komai shi bada wasa yazobahh,,,,,,,,,,, kuwa yanaso,,,,,,,, manya sushiiga maganar tunda wuri,,,, Kara matse fulon dake kirjin sa yayi,,,,,,,,,,,,,

Da mamakinta cikin farin ciki taji Yana cewa,,,,,,,,,, barin je insamu Abba yanzu Dan ABARI YA HUCE SHIKE KAWO RABON WANI littafin (sumayya Abdulkadir),,,,,,,,,, nikuma bazan Bari kizama rabon wani bahh,,,,,,,,,,,, kantayi magana diff,,,,,,,,, yakashe Wayan,,,,,,,,, dago wayan tayi sannan tabita da kyaya taccen murmushi,,,,,,,,,,,,,,

================

     MASARAUTAR       
            KANO

Kiliishii,,,,,,,,,, ne ta kishin  Akan wani tuntu dakagan shi kasan na Gidan sarauta ne Dan bako wani irin tuntu bane da'ake samu ako'inah,,,,,,,,,,,, kishin gideh take,,,,,,,,,,,,,,, wata budurwace Wanda Baza tafi kimanin shekaru ashirin da hudu ba 24 kykkawace sosae fara sol ga dara daran idanuwanta Masu rikita mutane tanada tsayi sosai Ga hips boobs dinta kamar wanda suke shirin fasa yar yaloluwar rigar dake jikinta,,,,,,,,,,,,,,

Magana takeyi cikin tashin hankali,,,,,,,,,,, wallahy momy Idan ban aureshi ba bazan Bari wata ta aure shi ba,,,,,,,,,,,,, idanu wanta ne yacicciko taci gaba da cewa,,,,,, inason sa inasonsa mumy kitaima min yanzu ko wayansa nakira baya dauka,,,,,,,,,, tun kafin nayi hauka kawae ku aura min shi,,,,,,,,,,, aiba shi ya haifi kansa zebi umarninku,,,,, ,,, na tabba ta idanna aure shi zansashi yasoni,,,,,,,,,,, duk wani girman Kai dayake ji dashi sayya sauke shi,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,, Kai niko bazai Soni ba Allah sanda nake masa ya ishemu rayuwa,,,,,,,,,,, magana takeyi kamar me tabin hankali,,,,,,,,,,,,,,,

Kiliishii,,,,,,,,,,,, Wanda randa ke kuna zuciyarta kamar tafito kasa tafado haka take jinta,,,,,,,,,, Dan taki jinin abinda zai bata ran tilon yar yar uwartata ,,,,,,,,,,,,, 

Kiyi shiru intyy nah Sai nasan yadda nayi mai martaba ya amince da auranku,,,,,,,,,,,, Danni ma hankali na zaifi kwanciya bazanso ace wannan dumbin mulki da dukiya yafita ahannun mu ba,,,,,,,,,,, ki kyale komai a hannu na Abdallah Dani yake zancehhh,,,,,,,,, Bai Isa ya wulakanta ki nabarshi bah,,,,,,,,,,, nide narufo musu kofa nace ta Allah bata Kuba Dan duk sharrin ku Abdallah yafi karfinku danshi da Allah yadogara,,,,,,,,,,

===============

Bayan wayan ta katse neh takira Amira sukasha hira,,,,,,,,,,
Wanda Har yasa amira yin mamaki,,,,,,,,,,,,  Dan tadade rabon da taji tana farin ciki haka,,,,,,,,, beb wai wani albishir ne haka najiki cikin farinciki,,,,,,,,, um akwae labarae dayawa kede daga school kibiyo gidanmu,,,,,,,,,,,,,,,,,
Kisha story,,,,,, OK beb ganinan zuwa,,,,,,, toh saikin zo,,,,,,,,,,,,,,,,, sallama sukayi,,,,,,,,,,, sannan taci gaba da yin game awayanta (cooking fever) tanasan game din sosai Dan Yana ebeh Mata kewa,,,,,,,,,, kasancewar duk yayyun ta Wanda suka fito ciki daya sunyi aure,,,,,,,,,,,,,,

Babban Yaron anty hajja ne yashigo Dan kimanin shekaru Sha daya,,,,,,,,,,,,, ummah wai kizo inji mamin mu tana falo,,,,,,,, toh cemata ganinan zuwa,,,,,,,,,,,,,,,,,

To be continued

Ur's
     Z33iiyyb3rw3r

BIBIYATA AKEYI         

Bismillahirahmanirrahim

Writting by
                © _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

.

6s Maryam where are u???? Ga page dinki ya danno❤😊


       Dedicated to u Maryam bawa luv u so much

Page 11

*
Fitah tayi tanufi falo,,,,,, Dan amsa kiran da anty take Mata,,,,,,,,,,,
  Yawwa,,,,,,,,, zoki tayani cire wannan kayan  gwamma in cirewa kowa nasa tun yanzu nahuta,,,,,,,

A'a anty gaskiya kibari kawae ba yanxu ba Danni bawani aikin da zanyi nagaji yanzu fah nagama yin break fast,,,,,,,
Juyawa anty tayi da mamaki takalli mama,,,,,,,
Mama yanzu haka kike barin yarinyar nan tayita zuba San jiki san ranta,,,,,,,,, Idan tayi aure to waye zairinga Mata aiki,,,,,,,, 
Turo baki gaba tayi Allah ni Sai indauki mai aiki,,,,,,,,, mai aiki???   Anty ta maimaita da mamaki dauke a fuskar ta,,,,,,,,
ehh aini ba yar aiki akakai masa ba,,,,,,,, saurin katseta Anty hajja tayi,,,,,,,
Kulll karna karaji kinyi zancen yar aiki Dan bakisan hatsarin dake dauke da daukan yar aiki bane,,,,,,,,,,
Kirufawa kanki asiri daga ke Sai mijinki aiki ba gagaranki zaiyi ba,,,,,
Kehh to in takaice miki,,,, wannan yar aikin ta gidansu,,,, ogan abbansu Mamii (yar Anty hajja )aita aureshi daga hajiya tatafi umrah tadawo tasamu ya aure yar aiki,,,,,,,,

Tabb aikuwa da anyi tsiya Dan bazan yarda ba saidai yazaba,,,, koni ko itahh,,,,,,,,,,, Kehh da Allah ai maganin Bari Kar afara ai sayya rabu dake Idan idansa ya rufe akanta,,,,,,,,,,,

Yawwa dama maganan wannan najeeb din damuyi dake,,,,,,,

Kinsan me ake nufi da soyayyar sirri,,,,,,,,,, saurin girgiza Kai tayi toshi zakuyi,,,,,,,, dan kinsan Idan muna hadawa da addu'a dole kuma,,,,,, muyi taka tsan tsan,,,,,,,,,,,
Kiyi yanda zakiyi kihanshi zuwa gidannan koma meyene kuringa yinsa awaya ,,,,,,,,,
Idanma yamatsu sai kun hadu,,,,,,,,, to yafi ace kunhadu agidan fatima (anty maman amal ) dannasan,, bazata taba bari kiyi wani abinda bai dace ba ,,,,,,, duk wani kula nasan zata bakishi,,,,,,,,,,,,,,

Kar ki yadda ki bar wata Baraka da agidannan za'a fahimci wani Abu,,,,,,
Abari a kullum Akan bakida wani mai sonki,,,,,,,, ko awaya yakiraki karki dauka acikin gidan,,,,,,,,,,

Gyada Mata Kai kawai tayi,,,,,,,,, tunani fal ranta shin Idan tace masa yaringa zuwa gidan anty bazai fahimci akwae wata matsala ba?????

Sallamar Amira ce ta katseta saurin Juyawa tayi tatafi da gudu ta rumgumeta tsamm,,,,,,,,,,,
Karasa shiga sukayi ta tsugunna harkasa tagaida mama cikin fara'a mama ta amsa,,,,,,, sannan tajuya tagaida antyy hajja duk da bawai tasanta bane Amma ta amsa Mata da sakin fuska,,,,,,,,,,,,,,

Cikin zumudi ta jata sukayi cikin daki,,,,,,,,,,,
Suna shiga Amira tayi saurin yaye rufin gyalen dake kanta na Dan kwalin doguwar rigar dake jikinta ne tajefa Kan gado,,,,,,,    beb bani infara sha plx,, barin inkawo miki ruwa,,,,,,, beb kibar ruwannan kawai nakagu in farajin labarin,,,,,,,,,,
Dawowa tayi ta zauna,,, beb badai angama lectures ba nop ba'agama ba kawai bazan iya jira bane Shiyasa,,
Toh ya skull?? beb banasan iskanci Idan kinsan bazaki baniba kawae intashi intafi,,,,,, tafada tana kokarin jawo veil dinta dake Kan gado,,,,,,,  saurin janye gyalen tayi meye haka Dan Allah daga wasa,,,,,, Toh kina wani jamin rai,,,,, sorry Toh nabari,,,,,,

Labari tafara Bata tundaga lokacin da wayannan mutane suka fara *bibiyarata* Har zuwa haduwansu da najeeb,,,,,,

shiru tayi sannan daga bisani tadaura dacewa beb shekara biyu kenan da lura danayi Suna *bibiyata* kuma na tabbata sunfi tsawon wannan shekarun kawai Dai lokacin Dana ankara ne,,,, sannan tadaura mata da mafarkin da tayi yau,,,,,,,,,,,, beb wallahi tsoro nakeji,,,,,,, kuma Allah inason najeeb sosai plx beb kiban shawara,,,,,,,,,,,

 Damamakinta tana dagowa saitaga Amira na hawaye,,,,,,, plx Amira kibar kukannan kinema min mafita,,,,,,,

Bawata mafita dazanne ma miki Dan da kindaukeni Kamar yadda nadaukeki baxaki boyemin wannan al'amari ba,,,,,,,,,,

Amma tunda hakane Naga alama Gara nayi baya dake,,,,,,,,, Dan nalura zamanmu kaman takura miki nakeyi bakyason hakan,,,,,,

Tana Gama fadin haka tazari jakanta da gyalanta da niyyar ficewa,,,,,, saurin shan gabanta tayi ta rumgumeta tsam,,,,,, tafara maganan cikin muryar kuka,,,,,,,,,
Beb wallahi ba haka bane banason insaku cikin damuwa ne ko kinsan cewa ko mama akwai abinda na boye mata,,,,, banfada mata cewa ana *bibiyataba* plx NAYI NADAMA liittafin ( *Aisha* *Ali* *garkuwa* ) bazan kara boye miki damuwa taba,,,,,,,

Dagota tayi sannan ta share Mata hawaye itama da share nata,,,,,,, komawa sukayi suka zauna Akan gado,,,,,,,,,,,,,,

Kiyi hakuri Dan na tabbata WATA RANA littafin ( *Asmy* *b* *aliyu* ) Sai labari kinji beb,,,,,,,,, Amma Ina tunanin gaskiya ba mugayen mutane bane,,,,,,,,,,, Allah Dai yasa wani Dan mai mulki ne yaganmu yace yanaso yasa ake gadinmu,,,,,,,,,,,, dukan wasa *hanna* takai mata,,,,,, kima daina tunanin haka kawai nabarsu a matsayin marassa aikin yi haka Dai suka ci gaba da tattaunawa Amma Amira ita Sam najeeb be kwanta mata bah,,,,,,,
Hankalinta yafi karkata da wayannan mutane,,,,, itama har takagu tasan suwaye ????

================

MG Abdullahi gabaki daya kwananan yarasa meyake damunsa,,,,,,,,,, yanaji akwai wani abunda yake shirin faruwa dashi,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,
Kullum zuciyarsa zafi take masa kamar Wanda ake huramai wuta kuma yarasa dalili,,,,,,,,,

Ummii ne tashigo tasameshi Ida nuwansa sunyi jawur gabaki daya tarasa Gane Kan dannata akwanakin nan,,,,,,,,,,,
Ibnii takirashi dagaowa yayi ya kalleta,,,,,,,,,,,,,,,,,

To be continued

Ur's
       _Z33yyb3rw3r_

BIBIYATA AKEYI         

Bismillahirahmanirrahim

Writting by
                © _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

Sadnaf nagode da addu'arki gareni!!!!!! Naji dadin fadan alkhairan da kikamun!!!!!!! Nagode luv u so much ❤😘

Page 12

*

Dagowa yayi ya kalleta da rinannun idanuwansa wanda suka sauya kala,,,,,,,,,,,,  zama tayi kusa dashi tasa hannu tana shafa gashin kansa ahankali tafara magana,,,,,,,,,,,,,,,
      Ibnii,,, kadena sa damuwa aranka banajin dadi kullum Ina ganinka cikin tashin hankali shiru tayi sannan   taja wani gauron numfashi,,,,,,,
Taci gaba da cewa,,
  Kokasan duk lokacin da naganka cikin damuwa da kunar zuciya nake kwana,,,,,,,,,,,,,
Kokasan damuwar ka tafi dagamin hankali fiye da damuwar kowa aduniyar nan,,,,,,,,
   Dan Allah kacire duk wata damuwa aranka,,,,,,, duk da nasan duk wata damuwarka bazata wuce akan yarinyar nan ba,,,,,,,,,
Kasani inaji ajikina wannan yarinya taka ce,,,,,,,, sau da yawa nakanyi mafarkin,,,,,,,,
Naga jikanuna da wata yarinya wanda bantaba ganin fuskar taba ko yaushe fuskar ta bata bayyana agareni,,,,,,,,, Amma a kullum idan Ina mafarkin nakan kasance cikin kwanciyar hankali,,,,,, nakanji hankalina ya kwanta da wannan yarinya,,,,,,,,
Koda ace na farka nakan kasance cikin farin ciki a wannan rana,,,,,,,
Sai alokacin yaji hankalinsa yafara kwanciya Dan duk yanda yakai da bacin rai mahaifiyarsa tasan magan ganun da xatayi su kwantar masa da hankali.

Ahaka tayita lallashin sa harsanda zuciyar sa yaji tayi sanyi Dan ita kanta taga canji daga ga reshi ,,,,
Fuskar sa ta sake bakaman dazu ba,,,,,,,
Bata Fita adakin ba sanda ta tabbatar yaci abinci sannan itama,, tafita,,,,,,,

================

Saikusan yamma amira tabar gidansu *hanna*  Bata Fita ba sanda ta tabbatar ta Bata shawar wari masu amfani,,,, har anty hajja tazata tafi sanda tabata tsarabar turare da kayan makeup,,,,,,
Wanda takawowa *hanna*  ta ebi wasu aciki tabata Dan yarinyar ta kwanta Mata arai tanada tarbiya,,,,
Taji dadin kasance war *hanna* tare da amira Dan Taji irin shawar warin kirikin da tayi ta bawa *_hanna_*

Har bakin titi taraka amira domin naiman abinda zai kaita gida ,,,,,,,,,, beb juya gefen dama,,,,,,,,,,,
daki gansu acikin wancan Yellow Range rober,,,,,,,,,
Saurin juyawa amira tayi aikuwa tarr tagansu Dan motar bame tinted bane,,,,,
Sanda takare musu kallo sannan tajuya ga *hanna*
Beb soldiers nefa,,,,,
Keh da'allah yaya akayi kika sani,,,,
Wallahi beb kiduba sarkokin wuyansu kigani,,,, oh oh baxan juya ba zasu gane muna kallonsu zasu zargi wani Abu,,,,,,,,,, ni tsoro bai taba barina na lura ba,,,,,, Allah beb inaji ajkina wani alkairi ne yake *bibiyar* rayuwarki amma kici gaba da addau'a Allah zai kawo Miki karshen matsalolinki basu dade awajan ba tasamu adaidaita,,,,,,,,, cike da kewar juna sukayi sallama tatsare adaidaita tatafi

Da dare yayi haka najeeb yakira ta suka sha hirarsu sasoai damashi mutum ne mai surutu sosai
Sai wajan shabiyu 12:00pm da anty tagaji da surutu tanasan yin bacci,,,,,,, tayi ta Mata fada kafin tamasa sallama takashe wayan ta kwanta cike da kewar juna bacci yadaukesu,,,,,

Da sassafe kamar kullum tayi shirin makaranta tagaida babansu kafin ta wuce makaranta,,,,
     Bayan sun fito daga lectures amira tace beb kirakani office din abba inkarbo aika hanna batayi Mata masu ba,,,,,,,,, Dan itama tagaji da zaman waje daya,,,,,,,
High court suka nufa Dan acan baban amira yake aiki,,,,, ,,, cike wajan yake da sojoji da kuma SS koba'a fada ba kasan manyan mutane ne acikin wajan,,,,,,,,,,,, ko mutum daya fa'a bari yashiga wajan,,,,,,,,

OK kinsande ni bazan koma ba,,,,, bakina kallanki da farin idoh ba ko balarabiya ce ke bazasu barki ki shiga ba,,,,,,,,,, dukan wasa amira takai mata banasan iskanci kawae muje ta baya mujira tafiyansu,,,,,,,,,,,,
Bayan tangamemiyan court din suka  nufa Bayan wani window dake cikin court din suka zauna wanda kana kallon window din kasan mai office din yanada matsayi Dan ya banbanta da duka windows din,,,,,

Zama sukayi awajan ba'afi minute da zamansu ba kunnuwansu yafara jiyo musu maganar dake kokarin tarwatsa kwakwal warsu gabaki daya zancen da'akeyi yafi karfin kwakwal war yara yan 19 year's

Gaskiya nayi iya bakin kokari na Amma abin yaci tura,,,, bamu da karfin dazamuja da mulkin sa,,,,,,,,,,,,,
Bamuda karfin da zamu iya kwatan wannan shaidu ta karfi,,
Duk wani shaida tana hannunsa yanxu abinda yafi kawae muhakura,,,,,,,,,

Haba!!!!!!!! Haba!!!!!!!!!justice wani irin zance ne wannan Idan Har muka bari wannan takardu suka futo,,,,,,,,
Da'samu babbar matsala

Dayan dake gefe ne yake zaune wanda daga ganin sa kasan babba ne akannan,,,,,,,,,,,,,, yajuya ya kalli gefen sa wai shin chief ba'abinda zakayi akaine ambar karamin yaron da dukanmu mun haifeshi Yana caja mana Kai,,,,,,,,,, karfa ka manta munbarka a shugaban sojojin kasar nanne dan musamu abinda mukeso,,,,, shiru chief yayi sannan daga bisani yace,,,,,,,,,, karfa ku manta ba'a karkashina wannan yaro yake ba shifa sojan kasa da kasa ne,,,,,,,,,,,, abu kadanne zai sameshi kasashe su mana gayya,,,,,,

Dayan wanda shi ba'abinda yace kawae ya daura daya akan daya Sai jijjiga kafa yakeyi  saida kowa yagama sannan yace Idan kun shirya saina raba mana alhaki dan ni nadade da shirya abinyi,,,,,,,,,,,
Kallonsa sukayi duka da Alamun tambaya,,,,,,,,,,,,,
Daga musu Kai yayi abinda zuciyoyinku suke tunanin shizan aikata kunsani duk wanda yashiga gonata kasheshi nakeyi ,,,,,,,

Amma yallaba!!!! Saurin katsesu yayi nasan tambayarku tayaya zan aikata kusani duk lokacin da nayi niyan abu saina aikatashi,,,,,,,,,,,,,,
Amma yallabai kasan yanayin tsoro nakasan Dubai bakaman na kasar nan ba,,,,,,

Ai mutum daya ne zai aikata hakan bana bukatar taro,,,,,,,,,,,
Saurin karbe maganan chief yayi,,,,,,   ,
Mutum daya ne zai iya kasheshi????? Ya tambaya cikin tsananin mamaki

Kudaina min wasu tambayoyi kawae kusa aranku cewa nan da kwana biyu duk wata damuwar ku tagushe ko labarinta banaso asake dagowa,, yafadi haka tareda daurawa da murmushi irin na manya

Amira ne tayi karfin halin jan hannun *hanna*  harsuka Fita acikin wajen bbu wanda yalura dasu,,,,,,,,
Abin hawa amira tatsara musu *hanna*  kanma saida taturata ciki sannan suka tafi kaitsaye gidansu amira suka wuce

Kwankwasawa amira tayi mai gadi yabude musu kofa,,,,,,,, haka taringa jan hannunta kamar wata tababbiya

Kaitsaye part dinta suka wuce kasan cewar babansu Amira yafi babansu *hanna*  dukiya sosai shiyasa kowa keda part dinsa,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,
Kuma yaransa biyar ne kacal da Mata daya uku maza biyu Mata macen shekaranta biyu daaure

Suna shiga daki tayi sauri tasa ki sannan tajuya zuwa ga *hanna* dake tsaye kaman gawa *hanna* *hanna* takirata ta jijigata Amma shiru daga hannu tayi tabata lafiyayyan mari Wanda ba shiri tadawo hayyacinta (kusan cewa Koda amakaranta kike kawarki tanemi kirakata wani waje toh kikira gida kifada kafin Dan kikan iya fadawa halaka su iyaye sunbar yaayansu akan suna makaranta) Dan gashi kusan haka tafaru da *hanna*

 *Hanna*  dan Allah mubar Wanda magana Dan fitowarta kamar rasa rayukanmu ne mu binneta kinji daga Mata Kai kawai tayi ammaa tasamu kanta da addu'ar Allah yasa kar suyi nasara akansa

To be continued

 _Ur's_
     _Z33yyb3rw3r_

BIBIYATA AKEYI         

Bismillahirahmanirrahim

Writting by
                © _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )


 _Asmy_ _b_ _Aliyu_
Nagode da addu'arki ki gareni Allah yabar zumunci

Page 13

*

Haka kawai ta tsinci kanta da masa addu'ar kariya daga sharrin su

Haka amira tayita kwantar Mata da hankali Dan tasan Abu kadan ke dagawa kawar tata hankali gata dasa damuwa,,,,,,,,  bata barta ba sanda taga tadan sake!!!!!! ,,,,,,,
   Ni wallahi amira abinda yadaga mun hankali Sai kace abinda yake faruwa a film bantaba dauka yana faruwa a zahiri ba,,,,,,,,
       Yanzu deh mubar wannan maganan barin duba mana abinda zamuci Fita tayi zuwa kitchen Dan dafa musu indomie Dan shi yafi komai sauki,,,,,,,,

================

Ina labarin najeeb ne??????

Yana katse wayan ya nufi falo a guje Dan fadawa mahaifinsu yaje nema masa aure,,,,,,,,,
Turus yayi tundaga bakin kofan falon zumudi yasa gabaki daya ya manta da babansu yayi tafiya,,,,,,

Murmushi yayi tareda sosa keyarsa  yajuya Amma ya kudirta duk randa akace dad yadawo maganar da zaifara masa kenan,,,,

Haka yashare sukayi tacin soyayya awaya shida sweety dinsa duk da rashin ganinta yana damunsa Amma,,,,, yakudurta gobe saiya sata a idanunsa,,,,,,,,,

Babban abinda ke damunsa dukda a'ido tana nuna masa tana sansa Amma abaki bata taba furta masa ba
Ya alakanta Hakan da kunyan da take dashi

Duk bata kasance bafula tana ba,,,,,
amma tanada matukar kunya,,,,,,,,,,,,,, ita cikakkiyar bahaushiya ce Wanda kana kallonta zakaga cikar zatinta na hausawa,,,,,,,
Da asalin kyawu irinna hausawa ya bayyana ajikinta

================

Wayan da take gefen sane ta dauki ruri!!!!,,,,, Koda ba'a fada ba yasan wayan da ke kiransa,,,
Wani irin faduwar gaba ne yake damunsa kuma yarasa dalili,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,
Hakanne yasa kallon yanayinsa captain Ahmad yafita daga office din zaiba shi privacy,,,,,
Dan MG Idan yana cikin wani yanayi baya bukatar kowa kusa sanin halinsa ne yasa Idan suna tare dashi suka ganshi a wannan yanayi suke bashi waje shi kadai??????

Captain Ahmad yazo Fita ya umurceshi da ya ajiye masa phone dinsa guda biyu,,
Da Wanda mahaifinsa ke samunsa da kuma Wanda yake talakawa masu complain suke samun sa,,,,,,,,
Sai akayi rashin sa'a dake phones din iri daya ne  ya'ajiye  Wanda manyan mutane suke nemansa,,,,
Ringing din da wayarsa keyi ne ya tabbatar masa da ba phone din dayace a ajiye aka ajiye bah,,,,,

Tsaki yaja sanda wayan tayi rurin ta tagaji bai dauka ba,,,,,,,,,
Sai da aka sake kirane sannan cikin nutsuwa yadauki phone din tare da picking din call din
Dan kiran daga mr presdent na Nigeria ne,,,,,,
Gaisawa sukayi cikin mutun tawa sannan yake fada masa sunada meeting da zasuyi a Dubai a burj al_arab kuma suna gayyatarsa tareda bukatan matakan tsoro

Haka kawae ya tsinci kansa da rashin son zuwa wajen Amma zaije kodan kare lafiyar al'umma

================

Sai karfe uku sannan amira takira driver yakaisu taraka *_hanna_* gida
Suka fito sannan sukayiwa Ammin su amira sallama har kofar gida suka kaita,,   sannan suka juya

Bayan shigar ta gida tayita kokari ta danne damuwarta, dan ko mama bata fahimta ba
Tun karfe tara najeeb yakira ta Dan hatta mance da abunda yafaru da rana hira sukasha sosai daga nan Sai kusan 10:30 sukayi sallama Dan anty hajja ta hanata wayan dare sosae.

Wayanta tasauka tahau bincike a iya bincikenta bata samu wata masaniya akan wannan mutumin da akeson kashewa ba,,, Haka bacci yadauketa da taradda din wayannan mutane

Baccine mai cike da mafarkai kala kala,,,,
Akarshe ne tayi mafarkin wannan mutumi wanda awancen lokacin tayi mafarki ya harbi najeeb,,,,
Ya gurfana agabanta yana kuka amma takasa jin abinda yake fada
Ahaka tafarka cikin tsoro Amma hankalinta baikai na wancen karan tashi ba waigawa gefe tayi taga anty hajja nata sharar bacci itada yaranta Mata biyu Aisha (mammii) mai sunan mama Sai halima Wanda taci sunan yayar babanta
Sauka tayi tanufi toilet tadauro al'wala salla taringa yi tana neman zabin Allah saikusan uku bacci yadauketa akan sallayan

Kiran sallan farko ne yatasheta tatashi takara dauro al'wala taga batar da sallah
Sannan tatashi anty Dan itama ta gabatar da nata sallan,,,,,,, koma wa tayi ta kwanta nan da nan wani bacci mai dadin gaske yayi awon gaba da ita

Kamar a afarki taringa jin muryarsa a cikin bacci komadda idanuwanta takarayi tarufe can kaman Wanda tatuno wani tayi saurin mikewa tayi cikin falo aguje tana ihu,,,,,

To be continued

 _Ur's_
     _Z33yyb3rw3r_

BIBIYATA AKEYI         

Bismillahirahmanirrahim

Writting by
                © _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

Page 14

*

Falo tayi da gudu, tana zuwa kuma tatsaya da mamaki dauke a fuskar ta,,,,,,,,,
Juyowa sukayi suka kalketa,,,,,,,,
Aikaman jira takeyi takarasa dagudu ta rungumeta,,,,
Cikin farinciki itama ta rungumeta,,,,,,,,
Muryar sane ta daki dodon kunnu wansu,,,
Oh ni tunda ba'a murnar ganina Sai in koma saurin saketa tayi ta riko hannunsa,,,,,,,
Yaya ba haka bane fah,,,, rausayar da kansa yayi!!!!!!!!
Toh meye Idan ba haka bah!!!!!!!
Kankantar da murya tayi,,,, yaya please OK ya wuce,,,,,,
Saurin sakinsa tayi tunowa da tayi bafah muharraminta bane,,,,,,!!!!!
Ankuma yafada acikin zuciyar sa,,,,,,,,,,,
    Zama sukayi nan tadi ya barke tsakanin yan uwan da suka dade basuga juna bah,,,,,,,
Hira sukeyi sosai har ma ta manta tanada lecture's
Can wayan ta ta dauki ruri,,,,,,
Tana kallan mai kiran saida gabanta ya fadi,,,,,,
Alokacin ta tuno tanada lecture's
Saurin daukan wayan tayi,,,,,,,,,,,
Beb wai me kikeyi a gida ne tun 9 fa muka shiga lecture's  kuma zuwa 12 zaiyi test ai batasan lokacin da taduro akan kujera ba,,,,,,
Daki tawuce tashiga wanka batafi 15minute ba tafuto,,,,,,
Shiryawa tayi cikin blue da red din atampha,,,,,
Bakaramin kyau tayi ba sannan ta dauko ribbom tayi parking kanta,,,, duk da gashin kanta bai cika tsayi ba Amma Idan tayi kitso yakankai kafadunta, cikan da kanta ke dashi ne yakan hana kallan tsayinsa sosai,,,,,,
Cikar da gashin ke dashi ne yasa da tayi parking yataso kamar Wanda tasa ribbom na acuci,,,,,,,,,,,,,
Dankwali tadaura sannan tadauko khimar dinta dogo sosai ta daura,,,
Sannan tafesa turare mai sanyin kamshi wanda saika matsa kusa da ita kafin kaji kamshin,,,,,,,,,
Takal minta ta dauko plat dake tanada Dan tsayi yasa tayi dass dass gwanin sha'awa,,,,,,,

Futowa tayi dauke da side back dinta mai tsadan ba jebbu ba,,,,,,,
Dan mama da yayunta na kokari wajen sayamata kayayyaki masu tsada,,,,,
Tsugunawa tayi tasauko phone dinta da tabari akan kujera,,,,,,
Juyawa tayi ta kalli kujeran da hameedah ke zaune,,,,, subhanallah wani irin kama naga sunayi da wannan yarinyar wanda bazasu wuce sa'anni ba Sai tsiran da bazaifi na months ba,,,,,

Tabbas suna kama saidai bambamcin da baza'a rasa ba,,,,,,,,,
6s muje koh,,,,,,
Muje inahh???? Skull mana kinsan ai tunda kinzo toh tare zamu,,,,,, Dan bawani uzurirrikan da zandauka,,,,,
Tashi tayi suka dugun zuma kitchen dan yiwa mama Sallama,,,,,, me nake gani badai wani wajen daku je ba,,,,
 *_Hanna_*  tayi saurin karfe zancen,,,,,,
Ehh mama school zamuje,,,!!!! Amma ai kyabarta tahuta yanxu fa isowarsu daga kano,,,,,
Ko ruwa batshaba balle wani abinci,,,,,
Zamuci a makaranta tafada tareda jan hannun hameedah,,!!!!!!

Saikusan 11 suka isa makarantar,,,,,
kiran amira tayi sukaje yanda take suka sameta,,,,,
Gaskiya Beb kuna kama da 6s dinki sosai,,,,
Harya wuce yanda kike fada,,,, saidai tafiki kyau tafada tareda kashe Mata idoh daya dukan wasa *hanna*  takai Mata kinfiye sa idoh kekam kinji jiki,,,,,,
Kyaleta kawai dannasan tafada ne kawai kowa yace kinfini kyau
Dan idanuwanki yafi nawa girma kuma kinfini dogon hanci
Cewar hameedah!!!!!!!
Dariya sukasa kede kawai kin tsorata da wayan nan idanuwan tanne amma bawani kyawun da ta fiki,,,,,

Beb bamu karya bafa,,,, lallai bakida hankali kikabar bakuwa da yunwa harara ta galla Mata wacece bakuwar,,,,,,,
Ninaga alama in muka biyeki Sai munrasa test dinnan,,,,,
Uhm kawai amira tace sannan suka nufi hanyan _barhakkk_ dake gefen hostels na school din danyin breakfast,,, 

Sanda sukeyi ordering kafin suka zaune tadi sukeyi wanda zaka rantse amira sundade da sanin juna da hameedah!!!!!!!!!! Dan duk su ukun bbu baya wajen surutu!!!!!!
Wayan *hanna* ce tadauki ruri jin kidan yasa tasan wa yake kira Dan ringing dinsa dabanne,,,,,
Daukan wayan tayi,,,, sannan tajuya gefe da gefe aikuwa caraff idanuwanta ya sauka akansu,,,,,,,,,,,
Saurin juyawa tayi sannan takara wayar a kunnenta,,,,
Hellow°°°°sweety
Na'am kina school ne????? Eh!!!!! Ina zuwa yanxu kijirani
Haka kawai ta tsinci kanta da faduwar gaba!!!!!! No plx karkazo,,,,, karnazo???? Dalili?????
Shiru tayi tafara kame kame '' ''''''''hmm dama nasani baki da wani abinda zakice nadade da fahimtar bakya sona nikadai nake hauka akanki,,,,,,,,
Tabbas kina shirin jefani wani hali Dan har ikika gujeni mutuwa zanyi plz karki barni nizan koya Miki yanda zaki soni Amma plx karki rabu dani yafada cikin sarkewar murya,,,,,,

Wani irin tausayinsa da sansa ne suka kara ninkuwa cikin zuciyar ta!!!!!
Mekaki fadi haka kasan Nima bazan iya rabuwa dakai ba
To meyasa bakyason muhadu????? Kijirani agidan anty Idan nafito a lecture's zanzo,,,,,,, OK bye luv u saurin katse wayan tayi dan bazata iya bashi amsa ba,,, tadaga wayan akunnenta tana murmushi,,,,,

Zuba Mata idoh sukayi kaman wanda tayi wani abun,,,,, meye hakan da'allah kun wani tsareni da idoh kaman tsoffin mayu,,,,, ko gizau basuyi ba sukaci gaba da kallanta hameedah harda karawa da tagumi,,,,,,,,
Amma cikin ranta wani dadi takeji na ganin yar uwarta tasamu masoyi,,,,,,,,,,,,,,,,,
Tsaki taja sannan taci gaba dacin abincinta,,,,,,,,

Waye shii?? Cewar hameedah najeeb tabata amsa atakaice yatsine fuska amira tayi "" ""sannan tace zaiyi yabari afusace da dago bangane me kike nufii ba cikin bacin rai!!!!!!!!!!

To be continued

Ur's
       z33yyb3rw3r

BIBIYATA AKEYI         

Bismillahirahmanirrahim

Writting by
                © _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )



This page is Dedicated to u___anty rash wish u success in your exams

Page 15

*

Ni na tabbata akwae wanda yarigashi kuma haka kawai zaizo yayiwa wani wucel aiba haka akeyiba
Cikin bacin rai *hanna* tace toh saiki mutu Amma aure kam na auri najeeb angama saikuje kuyita haukanku keda su
Tajuya gun waynnan mutanen ta maka musu harara,,,,,
Jan jakarta tayi tana shirin barin wajen
Saurin riketa hameedah tayi sannan takalli amira ku fahimtar dani mana har yanzu bawai nagane yanda kuka dosa bane

Juyar da kanta *hanna* tayi tarike kugu tana karkada karkada jikinta ida adole ranta ya baci
Dakyar suka shawo kanta ta zauna Dan Sanda amira tabada hakuri tukunna,,,,,,,,,,,,,,,,,
Labari suka fara bawa hameedah ba abinda suka boye Mata tass suka kwashe komai suka fada Mata,,,,,
Ai nan da nan idanuwan ta sukayi jawur,,,,, Kai Amma wannan Ammah nan anyi tsinanniya na tabbata da umma(mamar hameeda) tasani Sai ta Mata tass tass ai tasanta
Ke matar wan mahaifinki kike tsinewa,,,, ai wallahi Sai na Mata tsiya tunda ba yanxu zan tafi ba ai zata gane kuranta,,,,,,, adai Mata sassauci sukace tareda tuntsirewa da dariya,,,,,,
Amma kinsan me ni Allah banga laifin amira ba Nima inaji kaman akwae wani alkairi a tattare da waynnan mutanen tafada tareda kallonsu ta kasan idoh,,,,,
Harara *hanna* ta galla Mata da'allah malama rufa mana bakii!!!!!
Amma kinsan me kemafa banga laifinki na zurfafa ason najeeb ba danna tabbata gayan yayi danke ko akaya baki zaben jebbu!!!!!!

Kallan wayanta tayi subhanallah ke time din test yawuce,,,,
Wani test kum``````saurin rufe bakinta tayi da tafukan hannunta tunowa da tayi karyar data shirga mata dazu

Kallo mai cike da tuhuma *hanna* tayi mata,,,,,,,
Sorry Beb Allah narasa yadda zanyi kizo Skull ne nadau zancen jiyannane yahanaki zuwa shiyasa,,,
Dakiyi ma yafi haka,,,, ita kuwa hameedah banda dariya ba abinda take musu

Fita sukayi ta niyyar wucewa gidan anty  ai kuwa acan suka sami najeeb Dan zumudin ganinta bayan sungaisa da najeeb dinne,,,,,,
Suka shige suka barsu su kadai itakuwa anty murnar ganin yar uwarta hameedah yasa ta manta dasu,,,,,

Soyayya sukasha kaman bbu gobe kamar karsu rabu saidai duk wani Soyayyar su sukanyi ta cikin sanin yaka mata Dan basu taba goce hanya duk wani abinda addini yahana basa yinshi
Domin  albarka Soyayyar suke nema,,,,,,,,


================

        Dubai

Kasar dubai aranar yau tatashi cikin wani irin cikowar mutane sakamokon taron kasa da za'ayi gobe MG kokadan baysamu lokacin kansa ba danko lokacin cin abinci bai samu ba sakamokon yadda garin yake makill da jama'a yanata kokarin yadda zaikare lafiyan al'umma
Garin acike yake Dan manya manya sunfara suka duk wani waje da kuka sani nacikin Kasar Dubai acike yake Dan bakinmu na Nigeria  a wani katon estate yasauke a _emarr_ _sidra_ _hills_ _eatate_
Inda sarakunan larabawa kuwa sunsha karrama ansauesu a _arabella_ _town_ _houses_
Wanda wasu da yawancin su sunje ne Dan yawan bude idoh Dan dubai kasaace Wanda taci gaba sosai afadin duniya
Shirya sojojinsa kawai yakeyi inda bayaso asamu wata matsala awannan taron
Bakin Nigeria sun isoh Wanda suka hada da manya manyan yan shiyasa aciki kuwa hadda wanda suke neman rayuwarsa,,,,, shikuwa yananan yana shirin kare tasu rayuwar

Sanda yaje airport yataresu yasada su da masaukin su sannan yawuce zuwa wani wajan
Dan taran wasu shuwa gabannin
Dan kowani shugaba burinsa daya yakaaance MG yana daya daga cikin masu taryan sa awannan lokaci

Har kusan tsakiyan dare MG baisamu hutu ba dakyar su captain Ahmad sika yakiceshi Dan yasa mu hutu,,,,,

Futa sukayi suka shirya masa motoci 9 hadu na bayansa hadu na gaban sa Sai kuma tashi atsakiya,,,,,,,
Captain Ahmed ne yake tuki gefensa kuma daniel ne Wanda Shima MG ya yarda dashi sosai Dan yanada rikon gaskiya shiyasa Har yabarshi yashiga jikinsa sosai

Koda suka isa gida daniel ne yayi saurin fitiowa ya bude masa kofa fita yayi cikin takun sa nakasaita Wanda ko ba'afada ba kasan jinin sarauta ne

Kai tsaye cikin gidan yanufa,,,
Kowani soldier yazauna awajan tsayuwar sa captain Ahmed da daniel ne suka rufa masa baya hannu yadaga musu alamun su tsaya sannan yacewa captain Ahmed yabiyoshi akwae sakon dayakeson bashi bbu musu daniel yatsaya shikuwa captain ahmad yabishi abaya Dan karban sakon

Bayan shigansu ne daniel ya cije libs yarasa me captain Ahmed yafishi da MG yake nuna bamban ci atsakaninsu
Kuma hakan Yana matukar yimasa zafi aransa
Amma ya alakanta hakan da bambam cin addini dasuke

Abinda be saniba shine duk cikin sojojin MG yafiji da Ahmed duk da yafishi agirme dakuma matsayi hakan bai hanashi zama yayi shawara da, Captain Ahmed ba

Tunda yashiga yariga da yasan ummii tayi bacci to baibi takanta ba,,,,,,,,,,, abinda baisaniba shine ko karfe nawa zekai nadare ummii,,,, saitaga dawowanshi dake iya runtsawa sake labulen dake hannun ta tayi sannan taje ta kwanta,,,, koba komai ranta yayi dadi naganinsa cikin kwanciyar hankali,,,,, bandaki yawuce ya watsa ruwa baifi mintuna kadan da kwaciya ba bacci yadaukeshi,,,,,,,,,,

Asuban fari ya farka wani irin mummunan faduwan gaba yatashi da ita Wanda yarasa dalili wanka yayi ya shirya cikin kakinsaa mai fitar da ainihin kyawunsa da cikar zatinsa

Dakin ummii yawuce yasameta tana bacci baiso tada ita ba hakan yasa yajuya yatafi Amma irin wannan taron yaso ace yafita da addu'ar mahaifiya akansa,,,,
Sanda suka tsaya amasallaci musulmen cikin suka gabatar da sallah kafin suka nufi burj al'arab hotel din da za'a gabatar da taron

To be continued

Ur's
      Z33yyb3rw3r

BIBIYATA AKEYI         

Bismillahirahmanirrahim

Writting by
                © _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )


 
 _
 _This_ _page_ _is_ _Dedicated_ to _u_ :: *hajja* *_ceh_* * _kece * * _mutum_ * *ta* farko _datafara_ _bani_ _kwarin_ _guiwan_ _rubutun_ _littafi_  _tanks_ _alot_ _I_ _luv_ u _so_ _much__

Page 16

*

Sai wajan karfe uku 3:00 sannan suka bar gidan anty,,,,,,
Amira ta wuce gida suma suka wuce gida,,,,,,,,
Bayan isansu gida sunyi sallar la'asar wani sabon hira suka dasa
Kai sis wallahi najeeb ya hadu wani farr tayi da idoh duk farin ciki ya cikata anyabi abin sonta
Allah koh tace,,,, eh mana kunyi bala'in da cewa
Saleem ne yashigo kanin *hanna* anty hameedah wai kizo inji Ammah yafada yana kallon wayarta,,,,,,,,,,
Kai meye kawani zubawa wayarta ido da'alllah fice kabawa mutane waje,,,,,,
Kai sis kinfiya takura Ina ruwanki kokuma wayarki ya kallah zonan Saleem karba,,,,,,
Zuwa yayi ya tsaya medakayi da phone din sosa keyarsa yayI game yafada atakaice karba katafi,,,,, itakuwa *hanna*  murmushin dakisan waye Saleem tabita dashi,,,,,,,,

Ke wai ba Ammah ne kekiran kiba kikatsaya yatsine fuska tayi kyaleta kawai bawani akyaleta tashi muje,,,,,,,,
Nasan wani abin take nema Sai kiji dadin bata amsa,,,,,,,,,,,,,
Mikewa tayi suka nufi dakin Ammah
Suna shiga suka sameta itada yaranta rabi'ah da hafsat suna zaune
Afalo Sallama sukayi basusami amsawa hakan baida mesu ba suka zauna,,,,,,,,,,,,
Juyowa tayi ta kallesu gidan ubanki ne nan dazaki isoh tun safe bakizo kin gaishe niba,,,,,,
Maciya amana ko yanzu kuma dawani cin amana uwartaki ta aikoki,,,,,,

Ko uwarki bata isa tazonan gidan,,,,, tanuna batasan inanan ba,,,,,
Balle ke karamar marar kunya,,,,,,,
Iya bacin rai ransu yakai kololuwa wajan baci,,,,,
Hameedah ce cikin bacin rai tabude baki zatai magana s damke hannun ta *_hanna_* tayi da karfi kallon ta tayi ta girgiza Mata kayi kawar da kanta tayi cikin takaici na hanata ramawa da *hanna* tayi

Juyawa tayi ta fuskanci Amma kingama akwai Abu me mahimmanci da mukeyi tafada hadeda wani murmushi wanda Ammah takasa tantance namiye shi,,,,,,,,
Sake baki tayi Dan uwarki aibake nakira ba,,,,,
Rashin kunyan ki haryakai ki Har yakai agaban idanuwamu kiyiwa mahaifiyar mu raini,,,
Hafsat ce tatashi da niyyar dukanta,,,
Ammah tahanata kull karki tabata kibarni da uwarta zanyi ni,
Jan hannun hameedah tayi wadda ga baki daya ji take kaman ta fashe tsabar bakin ciki,,,,,,,,,
Janta tayi Har sunzo bakin kofa Ammah tace shegiya mai bakin jini,,,,,,
Saurin tura hameedah waje tayi tadawo cikin dakin wani kallon kaskanci tabi hafsa dashi,,
Wato kece Har zaki dakeni ko tabani wallahi saina miki shegen duka,,,
Sannan tajuya gun Ammah da gabaki daya al'ajabi yahanata cewa komai,,,,,,
Idan Har zaki iya duban idona kice mun mai bakin jini kamata yayi ki fara aurar da nagabanki wanda duk cikinsu bbu wacce bata bani sama da shekara ba tukunna kisamo bakin gori,,,,,,,,,

Tana fadin Haka tajuya tafice tabarsu cikin jimami
Samin hameedah tayi tsaye tana jiranta a bakin kofa,,, dayake taso biyota Amma takulle kofan,,

Murmushi tabita dashi saurin kawar da kanta tayi tafice fuuuuuuu
Binta *hanna*  tayi abaya Har suka shiga dakin mama ganinsu Ahaka yasa anty takirasu tana tambayarsu,,,,,,,

 *Hanna* taso boye Mata amma hameedah takwashe komai yafada mata ran anty yabaci Amma Sai ta danne kawai Dan yanada kyau tun yanzu afara koya musu yin hakuri kafin auransu

Ahaka yaya jalal yashigo yasamesu,
Kallon *hanna* yayi wai Ina kuka shiga ne kam tun safe,,,, gidan anty fa mukaje,,, shine ba gayyata yafada tareda zama kan kujera,,,,, yaya daga makaranta fa muka wuce,,,,, Haka suka zauna sukayi ta tadi Dan Har sunmanta da bakin cikin da Ammah ta durka musu

Sallar magrib ne ta tashe su sukayi sallar suka dawo akasake sabon hira,,,,,,,,,,,,,,
Saikusan 9:00 najeeb yakirata suka sha soyayyarsu sanda tafara jin bacci kafin sukayi Sallama takwanta Dan hameedah ta dade da bacci,,,,,,,,,,,,,
Irin mafarkin jiya data karayi ne yatashe ta,,,,
Tarasa me wannan mutumi yake nema da take kallonsa gurfane agabanta,,,,,,,,

Datarasa mafita kawae ta dauro alwala tagiba dayin nafila Har bacci yadauketa,,,,,,,,,,
Har ta makara a sallar asubahi Sai wajen 6:30 ta tashi tayi sallah
Tunda ta farka ta tsinci kanta cikin wata irin matsanan ciyar faduwar gaba
Gabaki daya Tanaji kamar akwai wani abunda ke damunta amma tayi duk iya tunanin ta tarasa dalilin damuwar tata

================

Taro yayi iya Taro Dan duk wani manyan duniyar nan sun halacci wannan Taro
Amfara gudanar da taro komai na tafiya daidai Ina tawajan MG haryanzu faduwar gabansa tsananta takeyi

Duk wani tsaro daya kamata awajan antanadar
Inda layin da MG yake zaune layin manyan mutane ne wayar sace tadauki ruri ganin yanda wajan yake a cike yasa yatashi dan amsa wayar, mahaifinsa ne yake kira yasa bazai iya kindauka ba

Kokarin fita daga wajan dayake yake niyyar yi soldiers suka taso Dan bin bayansa daga musu hannu yayi alamun su koma,,,
Bamusu suka tsaya inda captain Ahmed yabi bayansa,,,,,,,

To be continued

Ur's
     Z33yyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*
     

_Bismillahirahmanirrahim_

Writting by
                © _zaynab bawa_
_( z33yyb3rw3r)_

 *_Edited_* *_by_* _KSA_ _precious_ _Hajjah_ ce

*Dedicated to*   
    _*Ummi  Aysha* (haske Writter) novel d'in ki na mijina sirrina yayi sosai Allah ya kara basira da zakin hannu_

Page *17*

*
   Fita yayi cikin sauri dan amsa wayar da mahaifin sa ke kira.
Ga baki d'ayan sojojin suka bi bayan sa cikin sauri. d'aga musu hannu yayi alamun su koma. Bbu musu suka jah suka tsaya a inda suke.
   Captain Ahmed ne ya bi bayan sa
Dan ya san hatsari ne barin shi yafi ta shi daya.

Amsa wayar ya yi sannan suka gai sa. tambayar sa ya keyi da cewa.
   Yareemah...!!! Kana lafiya?" cikin murya mai cike da da muwa yace "lapya na klau abba, wani abin ne ya faru?"
A'a bbu babu komai ka kula da kan ka kaji ko?
Kuma na kira mahaifiyar ka tace mun bata san lokacin fitar kaba.
   Ya kama ta Karin ga sanar da ita, ai addu'ar mahaifiyar ma yana da Amfani kaji ni?"
 
   Yareemah yace "In sha Allah."

"To Allah ya kare ka daga sharrin ko wani irin halitta."
Ameen yace sannan ya kashe kiran.

Juya wa yayi zai tafi Sai ya ga daniel tsaye yana murmushi tare da sosa kyeya kaman Wanda yake neman wani alfarma.
   Kallon sa yayi sannan ya kawar da Kai yana kokarin mai da wayar sa cikin aljihu.

    "Sir MG please ina son magana da kai."
   Kallon sa yayi tare da cewa "Ehem! ina jin ka."

Yace "Sir Idan ba zaka damu ba mudan matsa tacan? ya nuna wani waje da bbu mutane ta cikin hotel d'in.

Kallon sa yayi batare da wani tunani a ransa ba ya nufi wajan.
   Sanda suka isah MG ya d'an jin gina ya lumshe idanuwan sa ba tare da ya kalle shi ba yace "Kai nake sauraro."

Duk wani abin da yake faruwa akan idon captain Ahmed ne.
   Amma da yake Shima ba abin da ya kawo a ransa yasa ya tsaya nesa dasu sosai.
    Ganin daniel na shirin ciro Abu daga cikin aljihun sa ne kuma ya nada tabbacin bindiga ne ya sashi fara shan jinin jikin sa.
   Ga shi Kuma idon MG a rufe yake. Da sauri ya fara kara sawa wajan da suke a tsaye.

Amma dake da rata a tsaka nin su kafin yayi rabi harya karasa fitowa da bindigan. magana ya farayi cikin garaji Wanda hakan ne yayi sanadin bud'e idon MG amma kafin ya bud'e ido Sai sau kan harbi kawai yaji a gefen cikin sa.

Karar har binne ya jawo hankalin jami'an tsaron da ke wajan.
   Bud'e idanuwan sa tarr yayi ya zuba su akan na daniel. Wanda ke wani irin dariyar mugun ta. A lokacin Idan kaga MG baza ayi tsammanin a kwai harbi a jikin sa ba. Sai dai Idan ka lura da yadda jinin kebin jikn sa.
   Wani irin huci yake fita da shi Wanda duk d'auri yar mutum a wannan lokaci Idan ya gan shi sai ya razana. Dan idanuwan sa sun sauya kala sunyi jawur.

Wani irin shaqa ya kai wa daniel. Kan wani Dan lokaci idanun daniel ya fara zazza rowa. ganin yana shirin hallaka shine ya sa ya kara d'aga bindigan ya sake masa a gefen kirjin sa.
   Ganin Haka yasa captain Ahmed cira bindigan sa Kan ya 'iso ya sakewa daniel ita a goshi.

A lokacin jami'an tsaro suka isoh wajan a kayi saurin rirreke MG da jikin sa gaba ki d'aya ya 6aci da jini. captain Ahmed ne ya kara so ya tallafe shi.

Ga baki d'aya gun ya cika da sojoji. kai kace wani taron sojoji akayi. ga baki d'aya hankulan su a tashe yake Ganin shugaban su cikin wannan ya nayin.

Motar tai makon gaggawa ne tazo in da yan jaridu sun cika wajan makil. kowa koka rin d'aukan abun da ke faruwa ya keyi.
   Nan da nan a kayi dashi babban asibiti dake cikin dubai. inda moto cin sojojin dake gaban su da Wanda ke bayan su sun Kai akalla mota sha biyu.

  Kai tsaye *_(mass general hospital bostoon International)_* aka nufa da shi.
   Manya man yan likitoci ne suka shiga theatre dashi. kokari su keyi na ganin sun ciro harsashan dake cikin jikin sa.

Ummii ne zaune a falo ita da wata 'yar aikin ta tana matsa Mata kafa. ji tayi ga baki d'aya ba ta cikin nutsuwar ta.
  Hakan yasa ta umarci d'aya 'yar aikin da take yan ka mata friut data kunna Mata TV.
Hankalin ta baya Kan tv d'in Amma labaran da taji a nayi ne yayi saurin jawo hankalinta wajan.

Idan ba kunnuwan ta karya suka Mata ba, taji a na cewa an harbi MG Abdullahi Abdul-Aziz lamido. Wanda a halin yanxu ba'a san yana raye koh yana maceh ba.
   Hawaye ne ya fara bin fustan ta bbu abin da take nana tawa Sai inna lillahi wa'innah ilaihi raji'un.! Wanda hakan ne yaja hankalin yan aikin ta suma ju yawa su kayi Dan kallon abin da ya razana ta. ihu d'aya daga cikin su Wanda ya jawo hankalin sojojin dake bakin gate da cikin harabar gidan shigowa.

A razene suka yiyo cikin gidan, dan ganin abun da yake faruwa. Kan Wanda tasa hanu akayi tana kwalla ihu su kayi suna tambayar ta abunda ya faru dan basu lura da ummi data dade da zama mutum mutumi ba a kwance. Wanda bata gane komai a lokacin. TV ta nuna musu da ga baki daya hankalin su ya Kai kololuwa wajan tashi.
    Ihu da sambatun sojojin ne ya dawo da Ummii han kalin ta tashi cikin tashin hankali ta musu umarni da su kaita a sibitin. Dan kuka yaki zuwa Mata gani ta keyi kaman karya ne.

   Fita suka yi Dan rakata asibitin motoci uku ne suka cika da sojojin Sai Wanda Ummii take a cikin d'aya. Kai tsaye asibitin suka nufa dan ganin abun da yake waka na....

To be continued

 _Ur's_
     _Z33yyb3rw3r_

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
                © _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

 *Dedicated* *to* *_ummi_* *_aysha_* (haske Writter )

Page 18

*
Wata irin faduwar gaba ne yake damunta ayau,     kuma tarasa dalili.
    Hakanne yasa ko waje batayi sha'awan fita ba.
    kasan cewar ranar asabar ce, bbu lectures, zama tayi kawai tana tunanin dalilin wannan faduwar gaban tata
     Can zancen mutanen na shekaran jiya yafado Mata.
   Addu'a tasamu kanta da kara yimasa na Allah yakareshi.
      Dakyar taya kice damuwaar aranta, domin kar hameeda ta fahimci wani Abu.

    Cigaba sukayi da hidimominsu kamar bbu abinda yake damunta,
Amma Can cikin zuciyarta damuwa ce sosai.
       Kusan karfe shadaya 11:00
  Tashiga falon babansu dake yana gida bbu office.
    Da Sallama Tashiga ya amsa Mata cikin farin ciki,
Nadauka yar tawa yau baza tazo taya abbanta hira bane, saboda akwai yar uwarta kusa da itah.

    Murmushi tayi sannan takarasa shigowa ciki, tazauna akasa kusada kafar sa.
     Dama wannan ka'ida ne duk ran asabar tana tareda mahaifinta tana tayashi hira "sannu da hutawa baba, yawwa sannu *hannatun* baba. 
      Murmushi tayi najin dadin sunan da baba ke kiranta dashi.
     Tad'i suka fara yi "irin" na d'iya da mahaifinta, cikin farin ciki da annashuwa.

Aljazeerah! Yake kallo, Amma hankalinsu gabaki daya yanakan tad'insu, tunda ta shigo yamaida hankalinsa kanta, danjin ko akwai Wata damuwa atattare da ita.

    Saurin daukan remote yayi "yana kara sauti, subhanallahi, Kai mutane babu Imani, wato duk wani mai gaskiya Sai sunga bayansa.

     TV take kallo haikam.
wanda tagama tabbatar wa wannan da yanxu ake fadin an harbeshi, A Aljazeerah"
    Shine Wanda ranar sukaji Ana zancen kasheshi,
   Batasan lokacin da hawaye yafara bin fustan taba, tsan tsan tausayin sane ya cika Mata ruhi,
Lallai wa 'yan nan mutane sun ciki azzalumai marassa imani.

    Juyawa baba yayi gunta dan yimata magana,
Tsintar ta yayi hawaye daya nabin daya.
      Juyawa yayi yaga yanda take kallo.
     TV takurawa idoh, sanin zancen da' akeyi a tv din yasa yayi tsammanin tausayi,
Yabata.

   Dan yasan itah! Mutum ce"  mai tausayi.
     Lallashinta yashiga yi"     sannan yace taje daki ta kwanta ,
Tashi tayi ta fita, yabita da kallon tausayi,

     Shiga d'aki tayi, takwanta rub da ciki akan gado, Sai zullumin wayannan mutane takeyi aranta.

    Hameedah ce" tashigo daka Mata duka tayi, ke Ina kika shiga inata nemanki,   saida ta'iso kusa talura da halin da 'yar uwar tata tashiga.
       Zaunawa tayi kusa da ita!! Taci gaba da Lallashinta, dan ganinta awannan yanayin tasan ambata Mata rai ne.

================

Koda zuwan su Ummii basusha wahalan shigaba.
     Dan akwai abinda sojoinsa suke d' aurawa adam tsen hannunsu. 
     Ganin haka yasa bbu bata lokaci suka cika cikin asibitin.

     Cikin dakin Theatre kuwa,,
Angano dayan harsashin rigar bullet proof dake jikinsa ta tare,
Inda dayan na gefen cikin sa " harsashin bulawa yayi ya fice.
    Amma dayake ba Kowani irin harsashi bane, anyi shine na musamman mai hade da guba yasa yaratsa jikinsa sosai.
     Gubar mai karfi ce.
   Koda kirjinsa da yake da riga Amma sanda wajan yayi shatin baki.

  Sun dauki akalla awah hudu akansa.

   Kafin sukayi iya kokarin na ganin sun kashe karfin Gubar.

    Saida suka kammala komai. lokacin awansu hudu da rabi da shiga theatre.

   Inda haryanzu maganin bai fara aiki ba, Sai yayi 1hour ajikinsa kafin yafara kashe Gubar.

    Lokaci daya suka gama aka futo dashi, ko numfashi bayayi.

Aka kaishi zuwa wani d`aki mai tsaron gaske.

     C I D camera ne takowani sako na dakin.

    Nan aka ajiyeshi.

   Dan zuwa nan da 2hours numfashinsa zai iya dawowa.

      Yanxu roban numfashi ne amaqale a hancinsa.
     Wajen dakin kuwa sojojine masu tsaransa birjik, tundaga gate din asibitin.
     Ummii kuma na kofar dakin da yake, addu'a kawai takeyi, kokadan tunaninta bai kawo ta "khira mahaifin sa ba.

================

     Mai mar taba ne zaune a faadaa.
    Wayar sa da ke hannun wani bafade ne, tadauki ruri.   
      Kallon sa sarki yayi alamun ya amsa, amsa kiran yayi tareda karawa mai martaba akunne.

   Sallama akayi ya amsa.
      Meh????? Yaushe???? A'inah?? Shine abinda sarki yace, inna lillahi wa'inna ilaihi ra'ji'un kawai yake nana tawa, wanda hakan yaja hankalin fadan.
       Rike kansa yayi dayake wani irin sara masa.
         Lokaci daya kuma yafara ganin duhu.

To be continued

 _Ur's_
      _z33yyb3rw3r_

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
                © _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )



 _Wannan_ _shafin_ _nakine_ *nafii* _nagode_ _da_ _yadda_ _kike_ _nunawa_ _liittafina_ _soyayya_
 _Kodan_ _ke_ _Sai_ _na_ _kara_ _yawan_ _pages_ 😜

Page 19

*

     Duk wani tashin hankali, mai martaba yashigeshi. Jin cewa d`ansa mafi soyuya yananan, rayuwa akwai ko babu.

       Ganin mai martaba, cikin wannan yanayi yasa akatashi fada Alokacin.

   Dakyar mai martaba, Ya tashi ya shige, sha shinsa.

     Kunsan yanda zance baya 6uya, barin ma amasarauta, mai girman gaske irin ta kana.

    Har yakai kunnan kilishi, alokacin da'akazo Mata da zancen suna tare da intisar da yayanta guda biyu.

       Affan Wanda bazaifi kimanin shekara ashirin da biyar ba. Da halima Wanda tayi aure yaranta biyu. Kanwar Affan ce"

 

     Bakaramin tashin hankali suka shiga ba, jin mahaifinsu na wani irin yanayi, wanda gab yake da tashin ciwansa.

     Nufan shashinsa sukayi, cikin matsanancin damuwa, basu jira anmusu isoh ba,

    "Shiga kawai sukayi"
   Nan suka ganshi ya kifa kansa,
      Affan ne yanufeshi cikin sauri, yarikoshi,

    Abbah meye yafaru???????
   Dagowa yayi ya kalleshi,
     Muhammadu je kayi mana tanadar mana jirgi zuwa dubai,
     Tafiyan   Karya wuce nan da awah biyu"
    Abba me zamu jeyi dubai??????
    Yareemah!!!!! Yareemah!!!!!!!    Kawai yake fadi cikin sarkewar harshe.

     Abbah"" mai yafaru da yaya yareeman??????
   

    An harbeshi!!!!!
  Fadin irin tashin hankalin da suka shiga ma bata bakine.
     Dan affan kuka yaringa yi kamar Wata mace.
        Intisar da halima kuwa kuka sukeyi kamar Wanda akace yamutu. 

     Kilishi" ne tayi kafin halin cewa, aibe kamata mutafi mu kadai ba,
      Mukira sauran yan uwansa sannan muwuce.

     Hakan kuwa akayi cikin Kan kanin lokaci akasanar da sauran 'yan uwansa. cikin awawin da basu wuce hadu ba duka suka hallara. Fadin irin tashin hankalin da suka shiga ma bata hannu wajan typing ne😭😭,
    Sosai suka shiga tashin hankali.
     Sai wajan bakwai na dare, kafin jirginsu ya daga. ✈.

================

    Anyi iyah bin cike , Dan gwano wayanda suke da hannu awannan aika aikan ankasa, Dan kokadan bbu Wata shaida da zata nuna hakan.

       Wannan aikin dole dasa hannun wasu manyan acikinsa, dama daniel yana raye ne to da akwai hanyoyin da zasubi Dan gano wayannan masu laifi.
      Amma tun harbin da captain Ahmed ya yi masa, daniel ko shurawa baiyiba ya mutu
     Amma a nanan an kara karfafa tsaro da bincike.

   Bayan kaman awah biyu da kaishi dakin hutu, wani likita yashiga dan dubashi,
       Alokacin kuwa hankalin Ummii yakai kololuwa wajan tashi, dan Har yanzu bawani gamsheshen labari gameda halin da d`anna ta yake ciki.

     Likitanne yaje shiga tayi saurin tsareshi, tana tambayarsa yasanar da ita!!! Halin da d`anta yake ciki , Idan ma yamutu ne kawai yasanar da itah"
     Mam" d`anki bai mutu ba yana nan araye mana iya bakin kokarinmu na ganin mun ceci rayuwarsa.
   

       Daga Fadin Haka yajuya.

   "Yashige dakin"

   Turus yaja yatsaya Ganin sa a zaune, kamar ba shine wanda dasu ko numfashi bayayi ba, kallon gefe da gefen dakin yafara yi Dan atuna ninshi ba mutum bane.

   "A iya saninsa wannan gubar yakan dauki tsawon lokaci kafin yasake mutum,  harya fara gane mutane.

    Fita yayi cikin sauri dan kirawo sauran `yan uwansa likitoci, Ganin yanda yafita a gigice yasa hankalin Ummii dasauran sojojin kara tashi.

    Ba'a dade ba yadawo da wasu likitocin guda uku abayansa.

    Ganin su cikin sauri sun shige dakin yasa Ummii fashewa da wani matsanancin kuka, basu dade da shiga ba _afeeya_ tashigo Wanda ita kebin MG da yaronta zasuje excotion egypt ne tabishi, Sai kuma wannan abun yafaru shiyasa tabar yaron acan tayiyo nan asibitin, cikin tashin hankali.

Farkon isanta sun hanata shiga ne, sanda takira ummi taturo captain Ahmed yashiga da ita!!! Ganin Ummii na kuka ne yasa itama tazauna ta fashe da nata kukan, bame lallashin wani.

       Sai wajan 6 :00am mai martaba suka shiga asibitin, lokacin da suka isoh sun wuce gidansu dake nan Dubai "wato gidan Ummii sanda suka biya bashin sallolin da ake binsu, sannan suka nufee hospital din.

  Ummii na ganin isowar mai martaba tatashi dasauri taje ta rungumeshi, sannan tafashe ta matsanan cin kuka, tana cewa sun kashe manashi, abinda take nana tawa kenan, bubbuga babanta mai martaba yahau yi, Dan Shima Idan yace zaiyi magana toh tabbas zai'iya yin kukan.
       Allah kadai yasan yadda yakeji, sanin dansa dayafiso yana cikin wani hali,
       Wani irin bakin ciki ne yatokare zuciyan kilishi jitakeyi kaman ta shakesu.

To be continued

 _Ur's_
      _z33yyb3rw3r_

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
                © _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

 *Dedicated* *to*

Page 20

*

    Isowar mai martaba ne yaje yasamu likitocin, danjin kwakkwaran bayani, aikuma sun samu labari mai dad`i dan an tabbatar musu da cewa Har ya farka, inda mai martaba ya nuna rashin gamsuwa da maganarsu, TV suka jona, nadakin dayake, aka nuno musu tundaga kaishi dakin harzuwa farkawarsa.

   Ba'afi awah d`aya da kwantar dashi, yafarka, harzuwa shigan likitannan, Ya fita yadawo da wasu likitocin suka zo dakyar suka samu, suka masa allurar bacci.
     Kasancewar maganin bai ratsa jikinsa ba. Kuma alluran da "aka masa jininsa nada karfi yasa basu dad`e suna" aiki ajikinsa ba ya farka.

   Gashi kuma, gubar haryanzu bata gama sake jikinsa ba, Kodaa lokacin daya farka bawai yagama sanin "a'inah yake ba.

     Wannan labarin ne yasa hankalin danginsa ya kwanta.
    Gida suka wuce, Dan mai martaba ya fahimci Ummii tun jiya bbu komai acikin ta.

      Dakyar ya lalabata suka bar aaibitin suka nufi gida, affan kadai suka bari acan, duk da intyy taso zama Amma, kilishi dake ranta abace yake tayi kirmushi shi tahanata.

      Suna isah gida mai martaba yaja hannun Ummii, Har kofar bandaki yaraka ta yace tashiga tayi wanka, ba gardama ta shiga, dan itama jikinta baya Mata dad`i ahaka.
 
    Bata d`auki tsawon lokaci ba ta futo.

    Nan ta samu Har ya had`a Mata tea mai katuro, zama tayi agefen gado, Mika Mata kafin tea d`in yayi nan ma bbu musu ta karba, tafasha sanda takai rabi kafin yadaga Kai, karasa mana yafada Mata, dagowa tayi ta kalleshi, tayi narai narai da idoh, hawaye yacika idon tapp, girgiza Mata Kai yayi, "ya kar6i kofin ya kara Mata abakinta, ba musu takarasa shanye sauran.

     Ajiye kofin yayi, sannan yajuyo da ita suna fuskantar juna, magana yafara Mata cikin harshen da tafi ji"  Amina kisan cewa wannan abun da yafaru da yaron nan bawai, rashin tsaro kokuma kulawa bane, yasa faruwar hakan.
    "A'a Sai dan Haka Allah ya kaddara, karki manta kowani dan adam da tasa kaddarar.
      Nisawa yayi sannan yaci gaba da cewa, ai mu abin alfaharinmu ne ace"  yaranmu duk duniya Ana alfahari da shi.
    Ba'irin taimakon da bayayi kingani kuwa ai addu'ar mutane ma kariya ce agareshi.
    A yau akace dannan ya mutu, mu iyayansa zamu zama abin alfahari ga duniya, mun haifi da kuma munbashi ingattaciyar tarbiya, Wanda hakan yasa yatashi da tausayi da kuma taimakon al'ummah aransa.

  Haka ya zauna adakin yayita kwantar Mata da hankali.

    Ganin sun shiga daki, sun dad`e ne yasa ran kilishi mummunan 6aci, dakyar ta "iya yin break fast tawuce daki, bata bi takan kowa ba.
   Koda sukazo komawa asibiti, cewa tayi kanta yana ciwo, sannu suka Mata cikin tausaya wa, sukace _afeeyah_  tazauna kodata bukaci wani Abu, cemusu tayi suje kawai bbu matsala da saketa,
    Sai hararan intisar takeyi takasan idoh, akan tazauna, kirmushishi tayi kaman bata ganta ba, dan jitakeyi kamar baza su "isa asibitin taganshi ba,

     Haka suka futo, suka dugunzuma Zuwa asibitin.

     Satinsu daya acan, MG yasamu lapya, Ya warware, Sai yar rama dayayi, yayi fari dama gashi bbu bambanci da larabawa, Sai yakara yin wani kyau sosai, Wanda yasa intisar kara yin kololuwa acikin soyayyarsa,

    Duk wani Abu datasan zatayi yafaranta masa rai takanyishi, Amma ko kallan arziki bata samu daga gareshi.
     Inda captain Ahmed ranshi baci yakeyi, irin yanda intisar ke shigewa ogan nasa, yasan akwai Wanda yakeso bayasan wannan kyautatawar da takeyi masa, bayason iyayen oganna shi su canja ra'ayi na jiran lokacin da suka eba masa,

    Kuma hakanne tafaru, dan ransu mai martaba da Ummii yana faran tuwa da irin kaunar da take nuna ma dannasu, shikuwa captain Ahmed ya yatqbbata tanayi ne dan riya.

 Gashi batada kunya kokadan bata dace da ogan saba, Dan ranan saida yaso marinta.

     Kusan watansu daya "a" asibiti kuma acikin satin sukesa ran komawa Nigeria, dan umarnin mai martaba ne hakan, inda su sun dade da komawa.

     Affan da intisar ne kawai suka saura da intisar taki yadda tabisu.

    MG ne zaune adakinsa, shida captain Ahmed.

     Daga idoh yayi ya kalli captain Ahmed, motsa  lips dinshi yafarayi wanda sukaci pink harsunfara kaman red, lokacin dana eba yakusan cika kuma bana tunanin za'akara min wani lokacin, captain ahmad tattaro hankalinsa yayi gabaki daya dan yasan yana wuya furta kalmomi musu yawa abakin oganna shi, Har inde kuwa yafara magana mai tsayi to maganar nada mahimmanci.

    " Iska ya furzar,  tareda shafa sumar kansa ya lumshe idoh, ya cikaba da cewa, ka tabbatar ka kira captain bala ya tabbatar ba'asamu matsala ba.

================

  *Hanna* ce suka fito a lectures, kowa ya gaji likis.
     Amira ce ta fara magana " inbanda jaraba irin na wannan malami ace monday za'afara exam Amma haryanzu yaki gama lectures, hmm ni wallahi nagaji nema, Ina gama exam kano zanbi yar uwata Sai Dan fara IT zandawo, bade tafiya zakiyi ki barni ba????? Amira ta amshe zancen, ahap Sai kuma kiyi, hameeda Wanda duk haushin su yacikata, itaba da karatu ba Sai shan wahaala, taama kasa tanka musu,

    Harsunzo tsallaka titin wajen school din Wata mota tatsaya agabansu.

To be continued

Ur's
    _z33yyb3rw3r_
*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
                © _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

 Wannan shafin nakune yan uwana, nakaina Allah yabarmunku, *Anty* *rashida* *Anty* *ummi* da kuma *Anty* *sadiya*
Zaynab bawa na matukar kaunar ku

Page 21

*

Har sun "zo dasu tsallaka" titi, wanda ke wajan makarantar su" Wata motace tatsaya, a dai-dai gabansu. Sunyi matukar "tsorata ganin gilashin motar bakine wulik, zuge gilashin motar akayi"  yaya jalal suka gani, hakanne yasasu sauke ajiyan zuciya, da mamaki fall aransu, na tambayar yaushe yazo, saurin bude bayan motar *hanna*  tayi tashige, sannan amira tabi bayanta, juyowa yayi ya galla musu "harara , shine zaku barmin wannan uwar rawan Kan a gaba???    Kayi hakuri yaya, Allah nagaji ne baxan iya zagayawa ba" juyawa kawai yayi, a dai-dai lokacin" hameeda ta iso" bude motar tayi tashiga.

    Amira yafaara kaiwa yasauke". Sannan suka wuce gida.
   Agajiye kowa ya shiga gida, wanka suka fara yi, sannan sukaci abinci, Sai Bayan sunyi sallar isha"  suna zaune, *hanna* ce" ta tabo hameeda ke ga yaya nan yazo, na tabbata zai amsa mana tambayoyin mu. Tashi sukayi suka nufi d'akin da yaya yake.

 
   Isowa kafar d'akin sukayi, *hanna* ce ta kwankwasa kofar dakin" shigo kawai yabasu amsa shiga sukayi da sallama suka sameshi, azaune yana chartting, zama sukayi akusa dashi, ta gefen katifar da yake zaune, yaya yaushe ka isoh, dazu" yabasu amsa atakaice.
       Yaya dan Allah kabar chartting dinnan magana mai mahinmanci zamu,  kallonsu yayi sannan ya gyara zamansa, ehem Ina sauraronku!!!!

     Yaya Dan Allah  akwai wani cin amana da mama da umman kano suka taba yi neh???? Kallonsu yayi cikin mamaki me yasa kukace haka????   Tambaya kuma akan tambaya kabamu amsa mana, hade rai yayi Idan baku futo kun min bayani ba ya ya za'ayi na fahimta???
Ammah na yawan kiranmu da dangin maciya aamana"  wani lokacin har ma cewa su adda hafsa da rabi'ah takeyi wai mu maciya amana neh"   wai suyi hankali damu, cikin bacin rai yadago ya kallesu, itah ammanneh tafada muku Haka???? Ehh!!  *Hanna* tayi saurin daga Kai, furzar da Wata iska yayi.

       Sannan yafara cewa "mu asalinmu yan garin bauchi ne, kakaninmu  asalin su yan dambam ne,  sunan kakanmu Mal Ahmadu da matarsa rabi'atuh, Allah ya azurtasu da yara guda takwas, inda yawancin su tun suna yara suke rasuwa, guda biyu kawai Allah ya zaunar musu Wanda sune baba na bauchi da kuma abba na kano", wato muhammadu shine baban bauchi, da kuma yusuf shine karami wanda ake kiransa da abbah.

     

     Mal. Ahmadu ne ya yanke shwarar tura babban bauchi, makarantar allo, sunyi yawo garuruwa kala-kala, inda akarshe suka yada dogon zango a bauchi, ganin zaman da yakeyi ne yasa ya nemi sana'a yafarayi, bayan sana'ar tafara karfi ne yasa ya yanke shawar shiga makaranta, alokacin yanada shekara sha daya yasa aka bashi aji hudu, sanda yayi shekara biyu sannan yagama makarantar primary.
   

      Sai alokacin yasamu damar zuwa wahaifinsa, "ya yi iya kokarin sa wajen yin sana'a, yasamu kudin da zaisaya wa iyayensa abubuwa da yawa"
    Alokacin yasamu kaninsa Dan kimanin shekaru takwas a duniya,
     Bai dade ba yasake koma wa" dan yin karatun secoundry nasa.

      Ahaka "yanayi yana zuwa kallon mahaifansa, Ana Haka Allah yayiwa mahaifiyarsu rasuwa, gaskiya sunji zafin wannan rashi Amma Haka sukayi tawakkali.

      Bata dad'e da rasuwa ba Allah yakarbi ran Mal. Ahmadu, sunyi kuka na rashin mahaifi, damuwarsu daya" yadda yusuf zai kasance"  dama bawani dangi ne garesu ba, Koda sunada su ma babu Wanda zai iya rike yusuf, dan kowa fama yakeyi da kansa.
      Haka yatattari kaninsa, sukayi cikin garin bauchi ya rungumi sana'a sosai Dan ganin ya ciyar da kaninsa.
   

        Ahaka yasamu aiki, awani shago nan yaci gaba da karatunsa, ba'a dad'e ba yasa kaninsa shima.
 Ahaka Har yagama karatunsa, bedade da gamawa ba" yasamu aikin koyarwa, dan kunsan zamanin da basai kanada wani ba" kake samun aiki, bezaya ba yaci gaba da karatunsa na NCE a lokacin da yagama ne albashinsa yayi kwalri, tara kudin yafarayi Har yasaya fili, Ahaka suka hadu da Ammah, Ya aureta, dafarko sunfara zaman lafiya, inda daga baya suka fara samun matsala,
Sai da yayi da gaske tafuto ta nuna masa ita kaninsa ne bataso, aikuwa anan Wata babbar matsala takara tasaowa, Dan ya nuna mata duk duniya bbu Wanda yakeso kamar sa,
Bakin hali kala-kala tafara nuna masa"
Ganin Haka yasa yayansa turashi garin kano karatu, kodan hakan da yayi ma bawai ya Mata bane, Sai kuma ta tada rikici Kan, duk wani dukiyarsa takare akan karatun kaninsa, dan Haka adole tasa shima yakoma karatu, Amma hakan baisa yafasa turawa kaninsa kudin karatu ba.

     Koda yusuf ya ga Haka sayya daina dawowa hutu, "Har Allah yasa yagama karatu, inda dama ya dade yana soyayya da umma (khadija), ba'ad'au lokaci ba baba yaje ya tambaya masa auranta, anyi biki masha Allah alokacin yaran Amma daya, Ahmad Wanda yaci sunan babansu tanada wani tsohon ciki takusa haihuwa.

       Abba yasamu lecturing a buk inda yaci gaba da karatunsa na masters"     ba'a dade ba umma tahaifi danta santalele "  Wanda yaci suna aminu sunan baban umman kanwarta akaturo dan tayata zama, daganan kuma taci gaba da zama awajanta.

     Irin halin Ammah ne yasa baba tafiya kasar waje karo karatu, kozai rabu da masifarta.
      Amma Haka yaje yadawo, saima abinda yakaru, hakanne yasa abba yanke shawarar, yimasa maganr karin aure" baiyi musu ba Amma yashaida masa baida wacce zai aura, shaida masa yayi ya dad'e yana masa sha'war kanwar matarsa tanada hnkali, da farko " baba yaki ganin cewa abin kunya ne ya auri kanwar matar kaninsa , Amma daga baya ya amince, ba'a samu matsala ba aka fara gudanar da biki, Koda Ammah taji labari ba'ayita da dadi ba"  dan cewa tayi tun yana talaka take tare dashi, Sai yanzu da yayi kudi, ganin ba Wanda yadamu da ita yasa ta lafawa, mama da baba suna matukar zaman lpy amma tana fuskantar kalu bale, daga wajan Ammah.

To be continued

 _Ur's_
       _Z33yyb3rw3r_

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
                © _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

Page 22

*
    Mama ta fuskanci kalu bale da yawa" awajan Ammah, kuma Har gobe tana kara fuskantar wani kalu balen.

      Farko tafara Mata da makirci da yawa" inda saita ebeh abinci da siyar, sannan kuma tace mama ne ta ebe, lokacin da suke su kadai, hakan bata faruwa Sai bayan ya auri mama, hakanne yasa yafara yarda cewa mama tana eba masa abinci gakuma satar kudi da ake yawan yimasa.

       Sosai suka fara samun matsala"   inda ita mama batasan meye laifin ta ba amma baba ya canja kwarai da gaske, Dan ko maganar ta ba sosai yake amsawa ba.
      Alokacin tanada cikin anty hajja, dake mama macece mai "sirri"    yasa bawanda ta taba fadawa, duk yataru wani abinda take gani bata magana, kuma iya kyauta tawa tana kokari wajan yiwa baba biyayya"   dan tabbas mama tafi umma hakuri.

     Ana Haka Har Allah yasa *Wata* *rana*  yadawo lokacin dawowarsa baiyiba, yadawo Dan yayi mantuwa ne, daga bakin kofa yahadu da Ahmad da kayan abinci niki niki, yana futa dasu,
     Ga mai abin hawa yana jiransa Ana loda masa kaya, zai dashi yayi ya tambayeshi Ina zaikai kayan???  Cewa yayi zai Kai gidansu goggo ne (gidansu kakaninsa), baba yayi matukar mamaki cikin hikima ya tambayeshi ko yaune farko, aikuwa kunsan yaro"  kuma bawai yasan meyake faruwa bane. Atake ya shaida masa ai yadade yana kaiwa.
Betsare yaron ba, Amma cikin zafin zuciya ya nufi dakin Ammah, abinda yaji ne ya matukar birkita zuciyarsa. Wato Ammah yaji suna tadi tadi da kawarta irin makircin da suke shukawa, Anan yaji shirin satar da take shirin yi masa na makudan kudi, kuma su daurawa mama Alokacin tace ta tabbata dole Sai ya saketa.

    Wani irin tausayin mama ne yakamshi, da tuno irin abubuwan da yayi ta Mata, Har zai juya yaga Idan be tabbatar wa da Ammah yajita ba" toh wannan sace sacen da takeyi bazata daina ba, bude dakin yayi ya shiga da Sallama, amsawa sukayi, cikin kid'ima Dan basuyi tsammanin ganinsa yanzu ba.
       Neman waje yayi ya zauna, tareda fuskantar su.
       Kiji tsoron Allah halima duk wannan abunda kikeyi dan kikori Aisha Wanda ita ta daukeki amtsayin yar uwa.
     Wannan abinda kikeyi bashi zaisani rabuwa da "itaba"   mai yasa bazaki riki kaddara ki dauketa amtsayin yar uwarki ba'   shiru tayi yayi ta mata magana mai sanyaya jiki hadeda wa'azi.
      Alokacin jikin Ammah yayi sanyi, amma cikin zuciyarata, haryanzu son ta kori mama yana nan.

     Sai bayan yafita kawarta ta kara zugata, Kan yacimata mutumci akan kishiya, Ana tadaura Mata aniyar zuwa gun boka, dan takori mama.

      Mama taga sauyi sosai awajan baba, Dan wancen lokacin ma tabari akan sauyin yanayi, yasashi canja Mata.

    Sosai baba yake nuna Mata kulawa, dan mama cikin ta bai hana Mata kula dashi ba yanda mama takasan ce, mace mai tsafta.

    Wannan kulawa ba karamin cin ran Ammah yakeyi ba, ko lokacin suna su kadai bata samu wannan kulawa bah.

     Bayan Wata biyu, ta haifi yarta mace, akasa Mata sunan umma, wato khadija Ana kiranta da (hajja), sosai baba ke nuna Mata soyayya, ma yarinyar dayake duk  yaran Ammah maza neh, guda uku.

      Haka rayuwa taci gaba da tafiya, lokacin inda yaran Ammah shida" uku maza uku Mata, yaya Ahmad shine babba yana aiki a lagos yanzu da matansa biyu da yara hudu. Sai yaya jabir da yaya unais da anty Maryam duk rana daya akayi auransu, Sai rabi ' ah da hafsat.

      Yaran mama uku tanada cikin na hudu, Anty hajja itace babba tanada yara uku, Muhammad shine babba Sai Aisha (mamii) karamin shine aslam, Sai maman amal itama yaranta biyu, Anty hundatu ne Wanda bata dade dayin aure ba, ta auri babban dan umma.

     Alokacin da aka haifi *hanna* ne kuma Ammah tadauki tsana ta daura Mata. 
        Alokacin ne tamata asiri, aka tura Mata aljanu Wanda bbu tabbacin akwai su ajikinta.
      Sai saleem da abba.
     Nisa wa yayi sannan yace kutashi kuje ku kwanta, dare yayi, tashi sukayi duk jikinsu yayi sanyi, danjin hali irinna Ammah.

     Dakin mama suka nufa, da Sallama suka shiga ganin momy sukayi zaune akan kujera, harara ta watsa musu daga Ina kuke???  Mama daga dakin yaya jalal muke, sauke ajiyan zuciya tasauke, shine zaku Kai dare Haka??? , kallon agogo sukayi, shadaya nadare 11:00, mama wallahy bamusan dare yayi Haka ba, kuwuce ku kwanta,

   Bamusu sum-sum suka wuce daki.

   Bayan sun shiga ne" *hanna*  tadauki wayarta ganin misscalls din najeeb tayi kusan 10,  ganin dare yayi ne kawai yahana ta kiransa dan rabonta da muryarsa tun safe,
Kwanciya tayi cikeda kewarsa aranta.

     Jarabawa suka fara sosai, kanta yayi zafi, kokadan bata da lokaci duk tarame.

   Gashi  ansa ranar auran Anty samha yarinyar umma.

      A ranar yaune MG yake shirin dirowa kasar sa ta haihuwa.
     Jirgi guda kasar Dubai ta bashi Dan tafiya da duk sojojinsa. Sai dai sukansu sunsan dasuyi rashin masu tsaro sosai, tareda Ummii da intisar da affan.

================

     *Masarautar* *kano*

   Shirye Shirye akeyi sosai na tarban *yareema* abdallah, kota Ina gyara masarautar akeyi, hatta garin kano sanda tasan da sunada bako inda, Har shugaban kasane yazo" dan taryansa,

      Karfe uku 30:00 dai-dai  jirginsu ya dira a Nigeria, garin kano.

     Dumbin taron jama'a ne suka zo taryansa, inda daga masarautarsu ma gayya gudane. Sannan ga governor da sauran Manya, hadda shugaban sojoji wato chief wanda afuska Sai farin ciki yakeyi sosai, azuciyar sa kuma da dadama daya kasheshi a wajan.

     Gabaki daya suka dugun zuma sukayi, masarauta.

To be continued

 _Ur's_
        _z33yyb3rw3r_

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
                © _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

Page 23

*
  Masarauta duka suka nufa" nan da nan kowani sako da lungu, na cikin masarautar ya dauka " *yareemah* ya isoh, dan ko ba'a fada ba yanda masarautar tadauki kidan algaitu da ko ina hakan ya'isa yasanar da isowar *Yareeema*".

    Cikin fada suka nufa kai tsaye" inda mai martaba da mukarrabansa suke jiran isowarsu".

  Sanda suka gama kwaasan gaisuwa, sannan suka nufi dakin da mai martaba da iyalansa suke cin abinci ".

  Aranan idan kaga fuskan MG koda bai kasance mai fara'a ba"  amma fuskansa ya nuna yana cikin farinciki".

     Sosai aka tanadar musu kalolin abinci", duk daman sababban abu ne agidan sarauta, amma nayau daban yake".

    Duk iyalan mai martaba suna tare awajan".

        Abinci sukeci cikin kwanciyar hankali da farinciki, irin wanda suka dade basuji ba.

    Dan sundau tsawon lokaci basu hadu haka ba.

    Bayan angama cin Abinci ne "  duk suka tare a falon mai martaba, tadi sukeyi Sosai irin na yan uwan da suka dade basu zanta ba".

     Kana kallon wannan zuri'a sai sun burgeka"   sun baka sha'awa irin yadda suke tadi kai ahade, dan awajan baza ka taba banbance cewa wannan dan wannan bane.

       Affan ne  ya kalli MG yace"  ya yareemah wai Yaushe wannan antynmu mai sa'ar tadazo ne????  Kallon sa MG yayi" cikin tsolaya ya kashe masa idoh daya, eh ai ya kamata musanta yanzu gaskiya, nan da nan kamar wanda suke jira ayi magana suka hau kansa kowa so yake koda hotonta a nuna masa, dan sun tabbata tacika mai sa'a, samun miji irin yareemah yana wuya" 

      Gaban intisar sai faduwa yakeyi, Cikin zuciyarta tana addu'a Allah yasa itace wannan mai sa'ar",

      Wacce naji sun kirata da anty surayya ne da karbi zancen, itace first born a yaran mai martaba.

     Yareemah yakamata ka duba wannan zancen, tajuya ta kalli duk mutanen falon, sannan tace "   ka kalli irin farincikin da muke ciki yanzu, kuma inada tabbaci da'akwai matarka a ciki, farincikin mu saiya fi haka, bakunan mu sayya fi haka budewa.

      Duk danginna bamuda burin da yawuce"  muga iyalinka kai kanka kasani duk zuri'ar mu babu mutumin da ya kaika soyuwa cikin rayukanmu.

      Kokasan iyayaenmu basuda burin daya wuce ace" yau sunga 'ya' yanka,  kokasan shiru kawai suka maka dan basasan abinda zai takura ka, amma bawai dan sun hakura da zancen auranka ba" shekarunka fa talatin da biyar 35 'yan mata sun kusa su fara cewa kamusu tsufa, sai irinsu affan, tafada cikin sigar tsolaya.

      Ganin kansa akasa yasa suka fidda ran samun amsa".

     Mai martaba dama yasan basuda amsar wannan tambayar, yasa bai samusu baki ba, dan sau dayawa yakan zaunar dashi yana masa wannan maganar"  amma amsar sa daya na wannan yarinyar, sujira da sauran lokaci, amma da mamakinsa gani yayi ya dago kansa da murmushi.

     Wanda duka falon Sanda abun yabasu mamaki, dan irin wannan murmushin yin su awajan sa nada wahala",

       Cikin zumudi wanda kwata kwata basusan shi da hakan ba yafara magana cikin muryarsa mai dadin sauraro baga mata ba har maza" wanda jinta yakanyi tsada",   kodan yasan hakanne yasa yake rowar jinta" ohow"🤷‍♀ idan wannan ne karkudamu matsalarku tazo karshe, nan da 1 to 2 month mai martaba zasuje nemamin aure" gaban kilishi ne ya fadi cikin razana da dubur bur cewa tace "  a'iinah???

      " Bauchi"      yafada batareda kawo komai aransa ba".

      Wuta ne ta daukewa intisar da kilishi"

    Inda duk dakin sai farinciki ya lullubesu gabaki daya sun rasa yadda zasusa kansu don murna.

      Affan harda taka rawa, inda mai martaba da ummii kuwa yanda kasan anmusu albishir da gidan al'jannah, Sosai baku nansu yaki rufuwa.

     Inda duk Abinci akeyi kilishi da intisar basa fahimtar komai.

      Halima ce ta zakud'o cikin zumudi sanda tazo gabasa taruko hannuwansa, *ya* *yareemah*   itace wannan wanda kake dakon santa kusan shekara goma,???    d'aga mata kai yayi "  yaya kaima Allah yasa tasoka kamar yadda kake sonta.

      Affan ne yayi saurin karbe zancen da'allah malama rufa mana baki, wacece zata kalli yaya tace bataso" ke kanki kinsan duk zur'ar mu bbu mai kyau da kwarjininsa, kallon ummii yayi cikin tsolaya yace"   aiko ummii wanda take cikakkiyar balarabiya bbu abinda zata nuna masa, duka ummii takai masa tana girgiza kai irinna shirmen affan.

         Kayyyah" affan barta tamun addu'a dan banida wannan tabbbacin akan zata soni, akwai mutanen da kyau da kudi da dukiya bai damesu ba, batasan koni waye ba balle tasoni.

     Amma inada tabbbacin arananda nayi asarar ta aranan rayuwata amfaninta kalilan ne, kuma har inde narsata toh bazan iyayin aure ba, yakarasa maganar cikin sigar da duk wanda yake zaune awajan sanda matsanancin tausayinsa yqamasu,

       Ummii har idanuwanta ya cicciko dan ita take zaune dashi ita kadai tasan irin son da yake yima wannan yarinya".

   Mai martaba ne cikin sigar kwantar da hankali yace "  *Yareeema* na karfa kamanta kai soja ne, mai juriya da kuma gwarzon taka, eyyah abba ata wannan fannin gaskiya ni rago ne.

     Yana fadin yatashi da niyyar futa, wanda bayar iyayensa da yan uwansa da dumbin tausayinsa, affan ne yayi karfin halin cewa yaya baka fada mana sunanta ba".

================

Nayi tafiya ya plz fans kuyi hakuri dan banida tabbacin kullum zakurunga ganin post dina harsai danawo zai dawo normal bye love uuuuu olll

To be contunieud

 _Ur's_
        _Z33yyb3rw3r_

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
                © _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

Page 24

*

   Juyowa yayi ya kalleshi sannan" da murmushin dake boye da damuwa  acikinsa".

     Girgiza kai yayi yajuya daniyar futa" mai  martaba ne yatsareshi"   yareemah " fadamun sunan surikata kaji".

    *"Hanna"*   wow"😍 halima tace" hadeda hada yatsunta biyu waje daya  sannan taware guda ukun amma sunan yayi ".

     Murumushi yayi kawai sanna yajuya ya fuce.

   Sojojinsa ne"  suka rufa masa wasu na gaba" wasu na baya"  suka sashi atsakiya, harzuwa wani tangamemen sashi wanda idan kagani, za'a iyacewa na mata hudu ne", amma gefen MG ne wanda yake rayuwa shi kadai".

    Gefe daya gida ne mai hawa biyu"   sainabiyun wanda suke jere amma shi plat ne mai matukar kyau duk yanda zan kwatanta muku kyawun wannan gida bamai yiyuwa bane, iya karshen kyau" gidan yayi kyau "  plat din ya nufa" wanda kofarsa  duk ta glass ne'  irin glass din da ko bullet baya 6ulashi".

    Wasu lambobi  aka danna ajikin kofar,  da'alamu kofar mai sucurity ce ",    kofar ne tabude inda wasu daga cikin sojojin suka fara shiga, sannan shima yashiga",  wani falo ne dan madaidaici mai kyawun gaske" komai na falon farine sol har daukan ido yakeyi",

      Daga dukkan alamu dai yafisan kalan farii".

      Har mamaki irin kyawun falon yakeban, amma nace bafa abin mamaki bane dan idanna yi la'akari da falon MG ne, kuma sanin kankune kunsan waye MG".

     Daki kai tsaye yawuce dan yin wanka ".

     Can cikin falon mai martaba kuwa, farin ciki ne da kuma tausayin *yareemah* da yabarasu dashi, sa6anin kilishi da intisar Wanda bakin cikine fall a zuciyarsu, intisar jitakeyi kamar zuciyarta zai futa dan bakin ciki ga wata irin kishi daya lullubeta, har cikin ranta ba karamin so takeyiwa *Yareema* ba"  ita kuwa kilishi zafin dukiya da mulki yakusan kubucewa ahannun su " amma duk yanda za'ayi bazata bari ya auri wannan yarinyar ba"   duk rintsi sai ta rabashi da itahh".

================

     *Hanna* sun gama exam lafiya", inda se shirye shiryen zuwa kano,  inda zuwansu yahadu da bikin anty samha da za'ayi sati biyu masu zuwa,  inda soyayyarta da najeeb sai karuwa yakeyi kullum idan basa maqale a waya toh suna gidan anty suna zuba soyayya, abu daya dayake damunta shine yanda najeeb yayi shiru da zancen turowa gidansu kokadan yadaina mata maganan,

     Yau sauran kwana biyu sutafi kano,  yaya jalal ne zaizo yadaukesu, sai shirye shiryen tafiya sukeyi.

      *Hanna* ce" tafito cikin sauri " daga alamu wani waje takeson zuwa, ammah ce azaune acikin gida, lokacin hanna tafuto wayan tane tafara ringing, hankalinta baikai kan Ammah dake zaune acikin gidan ba, daukan wayan tayi tana cewa, myn  gani fa ahanya inazuwa, gaban Ammah ne yafadi dan dagajin wayan da wani take"  kuma da alamu saurayinta neh, me hakan yake nufii kenan????  Ta tambayi kanta".

       Fucewa tayi cikin sauri dan zuwa gidan anty dasu hadu da najeeb, yaso ace shizai kaisu Ammah yasan hakan ba mai yiwuwa bane,   bbu yanda za'ayi iyaye subar yayansu yakaisu"  yana matsayin saurayi ba muharramunsu ba".

        Bayan isarta gidan anty,  tasamu najeeb ya dade dazuwa, sun dade suna hira, sweety" dagowa tayi ta kalleshi" kinji haryanzu bance komai gameda maganar turo manya ba ko???"

   Sunkuyar da kanta kasa tayi"

   Yaci gaba  da cewa"!!!!!

     Narasa mai yasa duk lokacin da zansamu abba da wannan maganar, sai wani abu yatsareni" kuma nakan dade bankara tunowa ba kuma akowani lokaci nayi tunanin zuwa hakanne take faruwa "   muringa yin addu'a dan jinakeyi kamar akwai wanda keson rabamu, narai narai yayi da ido" idan narasaki zan shiga wani hali, irin son da nake miki ni kaina bazan iya fadin sa ba",  wani irin tausayin kansu ne yakamata'.

      Murmushi tayi, addu'a ne yakamta muyi dan babu abinda yafi karfin addu'a".

      Shima murmushin yayi zanyi kewarki" amma zanbiyoki kano,  kinji sweety, umm lokaci yana tafiya,  hameeda tana jirana zamu shiga kasuwa,"  ok bari inkaiku"  no kabari"  kollon tuhuma yamata"   wai meyasa haka" hah"  nafarko idan na baki abu bakya karba" idannace ko makarantarku zanzo saikikii"  dan bakyaso kishiga motata??  Eyehh?? 

      Langa6ar da kanta tayi"  hava myn tayaya zan karbi abu ahannunka" ace a'iinah nasamo?? Kaikanka kasani dole sai an tuhumeni".

       Sannan zancen zuwa makaranta kuma" kaikanka kasan zancen duniya baya buya idan akaje akasamu, babanmu akafada masa fah,"   mai zai dauka yaturani karatu natafi soyayya??"

   jikinsa ne yayi sanyi"   yasan duk laipinsa ne, in sha Allah yakusan zuwa karshe kinji sweety,"

     Murmushi  kawai tayi amma aranta itama tana fatan faruwar hakan".

      Kallon agogon hannunsa yayi, yatashi yana fadin zantafi, abba zai aikeni" zanyi missing wannan kyakkyawar fuskar"  rufe fuskanta tayi daa tafukan hannayentaa,"  dariya yayi ya nufi kofar fita"    bazakayiwa anty sallam ba??"  eh kice mata na tafi"  fita tayi da niyyar rakashi har bakin motarsa tarakashi" sannan yatafi".

      Dawowa tayi tayiwa anty sallama, sannan tafito da niyyar wucewa gida,

   Turus tayi na ganin wayannan mutanen  masu *bibiyarta* sunyi parking motarsu,"  wata zuciya ce da tunkarota"  yau ko kasheta za'suyi saita tunkaresu".

      Cikin karfin zuciya ta tunkaresu"  gabanta sai faduwa yakeyi".

      Cikin wani irin mamaki mutanen suke kallonta ganin su take tunkarowa."

To   be  continued

 _Ur's_
       _Z33yyb3rw3r_

. *BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
                © _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

 _
   *_Ina mika sakon ta'aziyata ga feedoh yar ficika marubuciyar (matata gimbyata)narashin mahaifiya Allah yajikanta"._*
 *yakuma sa aljanna ce makomarta, idan namu yazo Allah yasa mucika da imanii" ameen*

*

Page 25

*
      Cikin mamaki suka tsaya kallonta,"  na ganin su take nufowa ".

     Har takai tsakiyan titin wani mummunan tsoro ya dira a zuciyarta".

   Juyawa tayi da sauri, da niyyar komawa".

      Tsayuwa sukayi suna kallonta," su kansu sunsan tayi kokari," shekara da shekaru, suna *bibiyarta*  kuma sun dade da gane cewa ta fahimci ana binta amma ko sau daya bata ta6a tunkararsu ba,"

   Sun sani tabbas yau sotakeyi tasan kosu suwaye??"

   Wata zuciyar ce takara tunzurota" shinke haka zaki zauna ana  *bibiyarki* bakisan kosu suwaye ba?? "

     Ko dalilin *bibiyarki*  dasukeyi yakamata ki sani wata zuciyar ta kara tunzura ta."

   Kara juyawa tayi ta nufesu, alokacin zuciyarata sai dar-dar takeyi."

   Ganin yanda suma suka zuba mata idanuwa ne" yasata tsayawa cak,"

     Alokacin wani mai mashin ya karyo kwata."

     Kasancewar anguwar bamai jama'a bane yasa abun hawa basu cika wucewa ta layin ba,"

 
      Irin 'yan isakan yara masuji da tashen girma ne, wanda suna kallon kowa suka kade bbu mai Iya daukan mataki, dan suna kallon iyayensu sunada kudi. "

      Ganinta atsaye a tsakiyar titin dake GRA kano road, yasa ya Kara karfin gudun _power bike_ din dan aganinsa rainin hankali ne ta tsaya atsakiyar titin,"

     Kanta ya nufa gadan-gadan da wani mugun gudu kamar me shirin tashi sama, "

     Hankalinta kwata kwata baya jikinta, wanda Ita batamasan da zuwansa ba,"

     Gani kawai tayi daya daga Cikin, wayannan mutanen yabude motar ya nufeta gadan-gadan Cikin sauri, "

   Wani Irin razana tayi,"  ganinsa ya nufota gashi takasa motsawa konan da can, "

      Gani tayi yana matsowa kusa da Ita, ya daga kafanshi kaman mai shirin yin naushi," sa hannu wanta biyu tayi ta kare kanta tana jiran saukan naushi kawai."

     Rufe idonta tayi Ruf!!    Jin shiru yasa tabude idanuwanta, budesu yayi dai-dai da lokacin da yasa kafa ya naushi mai mashin din dayazo dapp da Ita da niyyar kadeta,

    "iyah! Kacin razana ta razana, ganin mai mashin din da yake shirin kadeta, yayi gefe mashin din yayi gefe,"

    Wani Irin buguwa yayi, ganin hakan yayi" sanadiyar da yasa ta kwala Wani raza nenen ihuu!!

    Sosai tarazana ganin mutumin ko motsi bayayi alamun ya bugu, dayawa, "
   

        Juyawa tayi afusace wajan wannan mutumi,"

     Cikin tsiwa tafara magana."

     Aibashi yakamata kakasahe ba " nizaka kashe, dan bashi ne wanda kukayi tsawon shekaru kuna neman hallakawa ba"   

     Cikin kuka tace menayi muku ne kam da baza kubarni nayi rayuwata ba??"

     Wai kusuwaye mah??"

    Ganin yayi shiru yana kallon ta ne yasa tace" 

   Au nagane dan ku bakowa bane face azzalumai masu maida rayuwar mutum kamar ta dabba,

     Meye ka tsaya kana kallo na , ka kasheni mana, tafada Cikin karaji,"

    Cikin nuna girmamawa ga wanda akeyiwa magana da ladabi, kamar wanda yake wajan wanda yagirmeshi, yafara magana."

     Kiyi hakuri "mam"    hakkinmu ne kare lafiyarki, iya tsawon lokutan da akadauka   mana. "

   Duk Wani amsosin tambayoyin ki" k'ijiyesu kina gab da samun  amsoshinsu,  dan lokaci kalilan ne yarage"   tabbas nasan kinada tarin tambayoyi amma ki ajiyesu saura kiris" mutumin dazai amsa miki yana tafe."

    Ina so kisa aganinsa muka masu cutar dake bane."

    Yana fadin haka yajuya" zuwaga dayan, har lokacin ta na tsaye ko motsawa batayi ba" sai magan ganunsa ne suke mata yawo a kwakwalwanta,"

   Magana sukeyi amma batasan mai sukace ba taga ya tsaida adai-daita, ya nufota,

   Alama yamata da ta shiga bbu musu tashiga.

   Tana kallo yayi wajan wannan na kwancen itakuma mai adai-daita yaja suka tafi dayan ya biyo bayanta."

   Suna isa tacire five hundret, kojiran change batayi ba tashige gida da sauri-sauri gudu - gudu, ko sallama batayi ba ta bude kofan dake jikin gate din tawuce ciki."

    Direct d'akin mama tawuce, hameeda tasamu zaune tafad`aa jikin ta tafashe da kuka, Cikin kidima take tambayarta maiya faru??? "

  Bata iya bata amsaba sanda tayi kukanta mai isarta sai by buga bayan ta hameeda takeyi"

   
     Dakyar tad'ado ta fada mata duk abinda yafaru, Cikin sigar lallashi tace Kiyi hakuri natabbata bamasu cutarwa bane, kamar yanda suka fada, "

   Amma kikara kiyayewa, dan banji dadin tunkararsu da kikayi ba, ke kanki kinsan mahakurci mawadaci ne, tun da sunce lokaci kalilan yarage, muci gaba da addu'a har tsawon lokacin,"

   Sau da yawa nakanji ajikina tabbas ba masu cutarwa bane yasa hankalina ya kwanta Kiyi hakuri. "

   Haka tayita lallashinta har tayi shiru"   kuma ki canja mood dinki kar mama ta fahimta. "

      Juyawa tayi da niyyar daukan jakarta dan nunawa hameeda tsarabar da anty tabayar abata,"

    Karaf!!" idanuwanta yasauka akan mama wanda da alamu tadade awajan. "

  Kallon tuhuma take binsu dashi,"


  Lokaci daya idanuwansu yayi zuru-zuru alamun rashin gaskiya ya bayyana tattare dasuu"

   Shigowa tayi tazauna ta fuskancesu,"

   Mekuke zance akai?? " ta tambayesu, mutsu- mutsu  sukafarayi alamun basasan fadin abinda aka tambayesu" shiru sukayi nadan lokaci sannan tace" ba daku nakeyiba ne??"

  Mama daga najeeb ne "nan takwashe duka yanda sukayi dashi tafada musu,"

    Shiru mama tayi sannan tace Allah yakyauta " muci gaba da addu'a, tabbas wannan jarabawa ce ta ubangiji Allah yabamu ikon cinyeta"

     Su duka suka amsa da ameen. "

   Sannan mama tatahi tafuta" bayan tafita ne tajuyo ta kalli kofar dakin,"

   Bawai bata yarda da abinda tafad'a ba" amma tanada tabbacin ba zancen da sukeyi ba kenann,"

    Hasalima tun shigowar ta tabiyota ganin tashigo ahargitse ko lura da Ita datake zaune afalo batayiba, haknne yasa tabiyota danjin maiyafaru? Zancen da dataji ne yadau hankalinta yasa taki shiga. "

    Tadaura niyyar bazata gwada mata tajiba amma zata tsananta addu'a, kan Allah yakare mata d'iyarta daga kowani irin sharri."

     Ganin mama tafita yasa ta sauke ajiyan zuciya, hameeda ne takalleta sannan tace" sis bakya Kallon yakamata mufadawa mama?"

   Um Um ba yanzu ba dan kokadan banasan tashin hankalinta "

    Ok amma ki Kara kiyayewa, in sha Allah"

     Tashi sukayi suka nufi falo."

   Hameeda ce tace" mama kin kira momynsu amiran??  Nakirata amma kushirya kuje kukara tambayar ta da kanku. "

  Cikin sauri suka shirya suka nufi gidansu amiran."

   Dakyar momy ta amince data barta tazo amma sai satin bikin."

   Haka suka nufi gida bayaan da sukaso ba, dan sunso abarsu sutafi da Ita tare, "

   ================

  MG ne zaune afalonsa wayane sakale a kunnensa, kana Kallon sa za'a hango bacin rai karara a fuskarsa, ji nayi yana cewa"  Mekuke nufi da hakan kenan??"

   Cikin karaji naji yakuma cewa!!"

   Captain bala!!

 Karka yarda Irin haka takara faruwa??"

  Cikin rawar murya wanda ake waya dashi naji ya amsa da" yess sir,"  tsaki yaja ya kashe wayar, hadeda cillata a daya kujerar,

   Ya kishin gid'a a jikin kujerar hadeda lumshe ido, jiyayi an tabashi, a hankali ya bude idon yasaukesu akan Abubakar amininsa, tashi yayi ya zauna, sannan shima yasamu waje ya zauna."

    Abubakar ne yakara cewa"  Wato dabazaka dawo aurena ba kenan ko mai kake nufi?? "

  Eh!!" yanzun ma dan antakuarni ne da sai lokacin yacika, "

  Dakuwa anga dan iskan aminin ango"  Abubakar yace"

   Kaikasan dan kai nayita jawa iyayen yarunyar nan rai. "

   To ai gani nadawo, haka sukayita shirye shiryen yanda zasu tsara bikin Abubakar dan gidan waziri wanda za'ayi satin sama,

===+============

Amma ce gaban malam nakaranki hankali tashe
 

  _Kuyi hakuri da jina shiru kwana biyu sai jiya nadawo amma in sha Allah yanzu kullum zaku ringa ganina_

 To be continued

_Ur's_
    _Z33yyb3rw3r_

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
                © _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )



Page 26

*

    Washe gari da sassafe, Ammah tashirya da niyyar zuwa gidan malam,

  Bayan ta shirya tafito, tawuce gidan kawarta hajiya larai, wanda duk wani tuggu da muggan abubuwa Ita take koya mata, "

    Bayanin duk wani abinda taji jiya tamata, sannan takara da cewa, hajiya konawa zankashe arabata dashi,"  natabbata ba karamin mutum bane dan kinsan abinda malam yafada, har inde nayi sake asirin ya karye, toh mijin da zata aura samunsa nawuya, "

   Gaskiya bazan iya ganin zuwan wannan rana ba, wallahy yanda natsani uwarta haka natsaneta, intakaice miki hannafi tsanarta fiyeda uwarta,"

   Wata yar shewa hajiya larai tasa, haba kekuwa hajiya banfa sanki da sarewa haka ba, duk kin wani bi kin rikice akan yarinya karama, "

    Ammah ne tace bazaki gane ba ne hajiya, har wani lokaci nadaban fa babansu yake ware mata wai najin damuwowinta, komu matansa bamu samu wannan lokacin ba,"

    Wallahy tun lokacin da aka haifeta dana fahimci Irin son da yake mata nakejin tsanar yarinyar. "

   Kedai yanzu ki kwantar da hankalinki, halin malam saidai kifadawa wani dan shekara da shekaru yana miki aiki, baki taba Kallon ba dai-dai ba dan haka yanxu barina shirya saimu wuce,"

   Aitsabar tashin hankali kanmuje har na kirashi, mukawai yake jira,"

   Sai bayan tagama shirinta sannan tafito, a motar hajiya larai, suka shiga suka nufii kauyen," 

   Banisa ne dashi sosai ba, idan aka d'an futa agari yake,

   Bayan isarsu ne kaitsaya gidan malam suka nufa,"

   Dama ya dade yana  jiran zuwan su,"

   Bayan sun shiga ne amma ta gama koro masa bayanai, "

Shiru yayi nadan wani lokaci sannan yace, tabbas akwai wanda ke nemanata,"   kicin kidima Ammah tace malam arabasu, dan yadda uwarta ta kuntata min na auren mijina itama saina kuntata mata na ganin yarta agaban ta ba aure har abada, "

   Shiru yayi sannan yace, hakan mai yiwuwa ne amma dole sai mun dakatar dasu da yawan addu'o in da sukayi, kullum Cikin addu'a suke bbu rana bbu dare,

     Budar bakin hajiya larai sai cewa tayi alagafarta malama akaashesu kawai itada saurayin,   nikuwa araina nace wannan katon bokan basajin kunyan kiransa da malam shikuma yayita yake baki yana amsawa."

   Ammah ne tayi saurin katseta, A'ah"      baza'a kaahesu ba, idan nakasheta aiban cusawa uwarta bakin Ciki ba,  tazauna arayende uwarta taci gaba da ganin bakin Ciki, shikuma idanna kasheshi ai ban cusa musu bakin cikiba, gwamma suganshi araye amma yaki, auranta. "

    Kinga daganan na bata mata suna nace ya lalata tane yaki auranta, hajiya larai ce tayi saurin karbewa yanzunma waya sani tunda kince binsa takeyi wajan sa, shi bai taba zuwa ba."

   Cikin gamsuwa da shawarar su malam yace"    yanzu mufara raba tsakaninsu kafin muzo zuwa wannan stage din, "

   Wani dan magani yabata yace ta zuba masu a abinci, idan ta zuba kasala data sauka musu bbu mai iya tashi nafila acikinsu, acikn wannan daren yakeson yin aikin."

   Kar6a sukayi Cikin murna da ganin kaman burinsu yacika, suka zube masa kudi, suka koma gida,

    Direct gida tasauke ta, sannan itama tawuce nata gidan, "

    Tana zuwa kuwa tasamu inna kaltu tad'auura miyar dare,"

      Ko dar bata jiba ta aiki inna kaltu kasuwa, sannan tashiga tajuye, tarage kadan dan ta tabbata ba lallai su *hanna* da hameeda suci abincin darenba, dan saudayawa tana kallo da daddare abincinsu daban sukeyi,

     Bata damu da duk wanda zaici abincin ba, tajuye aduka,  itadai bazata bari 'ya'yan ta suci ba, "

  Yamma likis yaya jalal ya iso, zuwa gobe da safe dasu wuce, da dddare bayan anzubo mishi abinci, ya kalli *hanna* da hameeda dasuke zaune, ku sauko muci abinci yace tareda kawar da idanunsa daga garesu *hanna*  ta yatsine fuska yaya na koshi nikam,

   Wani kallo daya wulla mata, aitabaaan lokacin data sauko ba tasa hannu a abuncin, hameeda batajira anmata nata Kallon ba, tayi saurin sakkowa,"    Wani Irin dadi abincin ya musu wanda su kansu basusan dalilin hakan ba, kuma bawai abincin yawani hadu bane,  amma ku masu karatu basai nafada muku abinda ke Ciki ba😭. "

     Sanda suka cinye abincin tass sannan hameeda, takwashe kanukan zuwa kicin, hanna uwarsan jiki kuwa tayi d'ai-d'ai."

    Basu dade da cin abincinba suka kwanta, bacci sosai sukayi, adaran boka yafara aikinsa."

================

   Wani mutumi magani gaban likita hankali tashe, da police guda biyu acikin office din. "

   Magana naji yafarayi yana cewa"  tayaya za'ace ba'asamu Wani dalilin da zai nuna shaidan wanda sukayi hakanba, _jinayi kamar nasan muryan nan amma a'ina? 🤔 masu karatu kubiyoni dan musamo amsa amma nima nakasa tunawa_   police dinne yafara magana sir"  duk wani bincike munyi yanuna mana ba accident yayi ba bigeshi akayi, dan munsami mashin _power bike_ dinsa akasa bbu alamun kokewar Wani abu ajiki, gakiya i _ _asaured u that_ wannan dasa hannu aciki munakan _inveatigeting_ duk wani mai hannu zaisamu _punishment_ mai tsaurin gaske. "

   Yaja Wani _deep breath_ sannan ya kalli doctor, doctor" _please_ yaushe zai farfado??? "

    _Sooner_ in sha Allah inji _doctor_ ,yar buguwa ce _and then_ ya razana _so_zuwa nan da _few hour's_ zai iya farfadowa, fita yayi zuwa dakin da aka kwantar da yaron, sosai ransa yake bace, dan ya tabbata duk mai hannu sayya kasheshi,

Cikin yan minute's yakira shugaba police ya shaida musu akan su duba CCTV camera dake layin sukawo masa _result_  Cikin hour's suka gama hada komai suka kawo masa abinda yafaru alayin a wancen ranan."

 ===============

    Sai wajan 6:30 iyalan gidan alh muhammad suka tashi dawata Irin kasala, dakyar sukeyi sallah, kowa mamakin Irin wannan bacci yakeyi, dakyar su *hanna* suka samu suka fara shiri dan dawuri zasu wuce kano. "

===============

MG ne zaune shida Abubakar a farfarjiyan sha shunsa , sojoji sai shawagi sukeyi,

    MG ne yakara magana _in angry tonge_ , Wani Irin banzan zancen wannan har sai mun jira _sister's_ kafun a shirya yanda za'ayi _event_ din, haba *yareemah*  sunkussan zuwa dan yanzu inada tabbacin tasowarsa, mtswww Yaja tsaki tareda _hot n sexy eyes_ dinsa bai Kara cewa komaiba, dan
A rayuwar sa, _he hates_ acewai umarnin wasu zaibi, wayarsa ce tafara _ringing_  ganin kiran daga captain bala ne yasashi yin _picking_   abinda yadada masa ne yasa shi saurin mikewa zaune yarasa farinciki zaiyi ko akasin hakan,
Gabansa ne yahau dukan uku-uku."

To be continued

 _Ur's_
    _Z33yyb3rw3r_

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
                © _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

 *_Banida bakin yimuku godiya gaskiya naji dadin yanda kukeson littafinnan, da masu bina ta prvt nima inasonku kamar yadda kuke sona luv u all My fans_*

Page 27

*

   Karfe tara na safiya suka dauki hanyar kano, *hanna*  da hameeda na baya sai saleem dake gaba, a mazaunin mai zaman banza, yaya jalal kuma yana tuki, sosai sukejin dadin tafiyar dan ya jalal Allah yayishi mutum mai saukin kai, dajan kannensa ajiki,

    ==============

  Gabaki daya yarasa dadi zaiji ko kuma akasin haka shi kansa ya kasa ganewa."

    Shi kansa zaiso haduwar su amma da d'an sauran lokaci, "

    Juyawa yayi ga abubakar,"

  MG ne yace waishin amaryar tamu kam asalinta yar inace??

   Kallon mamaki abubakar yabishi dashi, "dan a'iya saninsa yareema bai iya tambaya ba, kuma koda waya sukeyi idan yabashi su gaisa baya kar6a saidai yace agaidata."

   Ganin Irin Kallon dayake binsa da shine yasashi murtuke fuska, wanda shi kanshi abubakar sanda yasha jinin jikinsa."

    Asalinsu yan bauchin yakubu ne yanxu amma suna zaune a kano tadabo, saidai wan mahaifinta nacan bauchin, _i knew it_ yafada acikin zuciyarsa, amma afili tabe baki  yayi,  kamar wanda bashi yatambaya ba, akabashi amsa ba, amma Cikin ransa so yake ya tambayi sunan babanta, dan Kara tabbatarwa, amma bayason raini, hakanne yasa yaja yamatse. "

   Tashi yayi yashigo daki, kan lallausan _bed_ dinsa yafada yana tunani, afili ya furta, _i knw now_ _she's big and matured enough_
Wani  Irin kasaitaccen murmushi yayi hadeda shafa gashin kansa."

  Haka kawai ya tsinci kansa dason ganin ta, _he wats to see her_ , koda ace batasan koshi wayeba, amma saiiya ganta."

  _Nougty girl_ yafada hade dayin wani kasaitaccen murmushin."

  Sosai yashigo niahadi aranar wanda duk wanda ya kalleshi saiya yi _noticing_ yana Cikin _good mood_

   ===============

   Sir gashi munkawo, _record_ na CCTV camera, umurtan daya daga Cikin _guard_ dinshi yayi, kan yamasa _playing_ ,  adan kankanin lokaci ya yi _connecting_ komai yafarayi. "

   Dai-dai wajanda take tsaye atsakiyar titi, yafara, dan camera tabaci daga dai-dai wajan tafara, dan basuga daga Ina tafuto ba, har wajan da dannasa yaso kadeta aka yi _hitting_ dinsa."

   Ganin hakan yasa suka dasa aransu cewa, anyaudareshi da mace ne suka aikata masa hakan. "

   Har za'a kashe, yayi saurin dakatar dasu, mai nake Gani kamar wandan soldier ajiknsa??"

  Zooming akayi aikuwa kaki yafuto baro-baro a jinsa wandon kaki ne sai rigan t-shirt. "

   Dayan police dinne yace, Sir wannan ba kakinmu bane dan soldier's dinmu Basa amfani da Irin wannan, bincike akafarayi na sojoji masu amfani da kakin."

    Cikin dan kankanin lokaci akasamo kuwa, cikin ladabi yace Sir, tawagar soldier's din MG Abdullahi abdulaaziz lamido ne kawai suke amfani dashi,

      Cikin firgita ya buga bench din gabansa, _i knew it_ nasani" nasani"  nasan wannan hatsabibin yaron bazai barni hakaba, amma _this tym i will make sure that i teach him an unforgetable lessons_ _you will regret treating me_  sai kayi danasani yafada Cikin karajii. "

================

    Tunda suka dauki hanya *hanna* tayi noticing ana binsu abaya, kuma tabbas tasan motar wannan mutanenne."

    Kusan 11 :30 tamusu a birnin kudu,"  inda suka tsaya a gidan kaninsu umma wanda yake zaune a birnin kudu, "  sun tsaya domin akwai aikar" da zasu karba suwuce da itah."

    Sosai suka samu tarba dayake ansan da zuwansu, abinci kala-kala akamusu, hadda snacks, da drinks da ruwan faro. "

    Matan kawu abdul nada kirki Sosai, haka tayita jansu da tadi kamar kannen ta, duk da hanna bawani saninta tayiba amma matar tashiga ranta Sosai,
Da yaranta guda biyu, Kareem da bazai wuce d'an shekara takwas ba sai k'anwarsa khadija anace mata (nana) sunan umma akasa mata."

      Sun fara cin abinci inda ya jalal Da saleem Da kawu abdul suna babban falo. "

   Sai *hanna* Da hameeda Da maman nana suna falonta, *hanna* bataci wani abinci Sosai ba gabaki d'aya tausayin mutanen wajan nanne ya lullu6eta."

   A yanda taga alamunsu tasan tafiyar bawai sunyita acikin shiri bane Tunda basusan niba, kawai binta sukeyi ko'inah."

    Kuma ayanzu haka ta nada tabbacin bawai sunci abinci bane, suna nan aqark'ame (arufe) a mota kamar wasu kaji. "

   Ganin maman khadija da hameeda sunmike dan zuwa yin sallah ne wani tunani yafado mata,"

    K'ara gyara zamanta tayi dake itah tana fashin sallah. "

     Sanda ta tabbatar sunyi ciki sannan ta ebi faro biyu Da sugar drinks sannan tajuya snacks a leda hadeda, naman kajin Da aka soya musu duk ta eba ta zuba a leda na sweet home tayi hanyar waje da sand'a kamar wata marar gaskiya, (nikuwa araina nace ai marar gaskiyar ce) "

================

   Karfe goma yayiwa, ammmah Da hajiya larai a gidan malam, danjin sakamokon aiki."

    Malam ne yafara magana, aiki dai amfara amma haryanzu ba'a karasaba, dan basu kadai sukeyin wannna addu'ar ba, dan haka yanzu saimunbi duk maihanu aciki mun tura masa aljanun Da zasu sasu kasala, shima kuma wannna aiki nadaukan lokaci dan, saimunyi yarjejeniya Da aljanun,"

     Yanzu haka ina bukatar kudi masu yawa dan gudanar Da aikin,.

    Hajiya larai ce tayi saurin cewa kaman nawa malam?? "

    Zaku iya kawo dubu dari dan wannna ba karanim aiki bane."

     Zufa ne tafara ketowa ammmah dan batada hanyar Da zata samu makudan kudinnan. "

     Cikin rawar murya tace malam anama sassauci mana."

   Ai iya yanda za'a bukata a aikin kenan. "

   Haka su amma suka tashi suka tafi jiki babu kwari,"

  Acikin motane hajiyaa larai ke ce mata, kiyi yanda zakiyi anemi kudinnan, ko k'adararki kisayar inyaso na ciki miki sauran, ai matsalarki tawace. "

    Ahaka ranta yadan samu ya sanyaya, subhanallah wai akan cutar Da dan uwanka sai salwantar Da duk abinda ka mallaka dan kuntatawa wani, wa'iya zubillah Allah yakaremu."

    Ahaka suka tsayar da zance bayn sun sqyar sukoma gidan malam. "

     To be continued

Ur's
   _Z33yyb3rw3r_

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
                © _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

  *Maman manal Wannan baby na wahalar damu dayawa 😜Allah dai ya futo dashi lpy, saura kuma kice na miki terere* 🙈😜😉

Page 28

*

   Futa tayii ahankali kamar wata marar gaskiya."

   Hange "   hange"   tafara can " sai ta hango motarsu awajen can dan nesa Da gidan."

    Nufarsu tayi Da gwarin guiwa, amma duk da haka gabanta yanata faduwa dar-dar.

   Tana isah"  bakin motar ta bubbuga glass din, ahankali suka zuge, kara hade rai tayi sannan tadauko ledar Da mika musu, ba musu dayan ya karba wanda yawanci shi yakeyin _driving_ din _car_ din. "

   Kara turnuke fuska tayi, sannan tace kudaina zama Da yunwa, ta dalilina gwanna idan zaku ringa futa kuna neman abinci ku futa."

   Tana fadin haka tajuya. "

   Binta sukayi Da kallon mamaki,

   Juyawa yayi ya kalli dayan sannan yace, captain bala yarinyar nan nada abin mamaki."

  Yadda kasan oga data murtuke fuskar ta shima haka yake, an hadu an dace sukace hadeda kyalkyalewa da dariya, bude ledan sukayi, gaskiya yarinyar nada kirki, wato hartaji tausayinmu. "

    Dama yunwa sukeji, take suka fara cin abinci."

   Karfe biyu suka fito dan wucewa kano, sosai sukayi kewar maman nana mace mai kirki. "

   Sun dau hanya, sun kai wudil najeeb yakirata, tayi mamaki nasanin cewa yasan dasudau hanya amma ko saudaya bai kirata ba."

     Sauke ajiyan zuciya, tayi sannan tayi picking call din,  hira sukayi sosai, har ta manta Da yaya jalal a motar. "

    Haka kawai yaya jalal ya tsinci kansa Da bakin cikin wayar da takeyi, shi yasan ya dade yanason *hanna*  amma kuma yarasa dalilin dayasa har yanzu yakasa furtawa."

    Saida suka shiga garin kano sannan sukayi sallama da najeeb, alokacin ran yaya jalal yakai kololuwa wajen baci, yayi kucin kicin ya hade rai,

================

  Wannan mutuminne wanda haryanzu bawai nasan waye bane, yadaga waya yana kira da alamun wani yake nema." 

   Can aka dauki wayar, cikin firgici yafara magana, chief sanda nace ma a airport mutada bomb yamutu ahuta kukaki, gashi abinda nakeji yafara, faruwa. "

   Yanzu Haka dan gidan minister yananan a asibiti yafara daukar fansa."

   D'azu yakirani yake shaidamin, cikin wayanne naji ankatseshi, ya'akayi har yasan mune muka aikata??" shima ya fada cikin tsoro, Yanzu abinyi shine, duk kai musu waya muhadu musan abinyi, tun kafin kwabar mu tayi ruwa, nan Da zuwa _week_ duk muhadu a abuja. "

   Cikin kid'ima ya amsa Da _yes_ kawai, yana gama wayar ya cire hula duk ac dake falon amma gumi na tsatsafo masa."

    Haka kira yayita shigowa wayarsa kowa cikin tashin hankali yake tambaya danjin, cikekken labari. "

   Ahaka dai suka tsaida magana akan zuwa _next week_   zasu samu yin meeting dan samun _solution_."

   Akarshe ne yakira wani awaya, bayan ya dauka ne yafara ce masa, "

    Inason ka samomin tak'aitaccen _history_ MG Abudullahi abdulaziz lamido ne."

   Duk wani wanda yasha feshi, Inason sani koda jaririyar da aka haifa a family din akawo min sunanta Da kuma pic din su, zuwa nan da _3days_  banji mai akace ba yasauke wayar akunnensa. "

     ===============

   Sai yamma likis suka shiga garin kano, kowannensu agajiye yake, gashi kokadan yaya jalal baya gudu amota."

   Kuma k'arin abinma, bacin ran dayake ciki yasashi k'ara saibi. "

   Suna isa cikin gidan ko gaisawa da umma basuyi ba suka wuce part din 'yan mata yanda dakin anty samha da hameeda yake."

    Suna shiga agajiye suka zube kan gado, sis wai meya batawa ya jalal raine a mota?? "

Ki kalla fa ko magana yakiyi."

 Damuka iso ma ko kallon mu baiyiba yafice yabar motan. "
    Ohonsa nikam, tana fadin Haka tashige ta dauro alwala, bayan tafito *hanna* ma tashiga tayi wanka, bata damu Da yamma Da tayiba, ta d'ane gado sai baccin gajiya, dama rabonta da irin Wannan tafiyar tun tana yarinya."

    Bayan hameeda ta idarda sallah ne itama tabita gadon, nan danan bacci mai nauyi yayi awon gaba dasu. "

   To be continued

 _Ur's_
     _Z33yyb3rw3r_

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
                © _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )



 *this Page is humbly dedicated To u maman manal yhur such a nice an wonderful person luv u so much* ```nima inasonki kamar yadda kike sona``` ```muna mugun tare```👍

Page 29


   Basu suka tashi daga bacci ba, sai kusan bayan magrib. "

   Umma batsan da dawowarsu ba dan tajira har tagaji kuma takira waynsu *hanna* ba'a _picking_   yaya jalal dama ransa abace yake shiyasa yana isa yakashe wayansa, saleem kuma bayansa yabi suka shige daki."

    Kusan _eight_  8:00 wata irin yunwa tatashi *hanna*. "   gani tayi hameeda tawani baje sai baccin take sharar bacci."

   Dak'ar k'arewa tayi ta sake mata marii, a _back_ dinta sanda ta tashi zaune bbu shiri. "

   Ke da'allah yunwa nakeji." shine dan rashin mutunci sai ki dake ni banza kawai, tafada hadeda komawa baccin ta. "

  _Please sis  wake up am terribly hungry_ , bakisan kofa ba kenan, tafada atakaice."

   _But i said am srry_ *_hanna_* tace had'eda langa6ar Da kanta, banza marar mutunci tafad'a had'eda mikewa tayi hanyan futa, ai *hanna*  dataga ba sarki sai Allah kuma tafiya zatayi ta barta. "  a arba'in taduro akan gadon tabi bayanta."

   Afalo suka sami Umma tayi tagumi, ai Da gudu *hanna* tawuce hameeda tafad'a jikinta. "

  A razane Umma ta juya jin mutun ajikinta, ai tana ganin *hanna*  cikin murna ta kankameta ajikinta, sai can ta sake ta."

   Ba kunya *hanna*  ta gyara zamanta dere-dere akan cinyan Umma, kod'od'uwa Da ita sai wani zuba mata shagwaba take zubawa kamar 'yar goye. "

 Tsakin da hameeda taja ne yasa hankalinsu yakai kanta datake tsaye."

   Ware mata hannu ummah tayi, sannan tasaki murmushi ta shige jikin Umma. "
Umma Haka Allah yayita dasan yaranta da kuma jansu ajiki."

   Ture ture suka fara kamar wasu yan biyu,, dariya kawai Umma keyi musu, dan yanda takejin hameeda Haka takejin *hanna*  kokadan bata tabajin banbanci akansu ba, hasalima dukansu da ita suke kama. "

   Yaran ummah biyar ne Allah ya azirtasu dasu, babban danta ya auwal shike auran anty hindatu yar mama, sai me bi masa yaya jalal, daga nan sai anty samha wanda za'ayi aure tagana degree dinta a buk." sai salman wanda hameeda ke bi masa, yagama degree dinshi agana yana service, kunsan yanayin karatun mu bad'aya dana muba dan anty  samha tarigashi shiga da shekara daya amma tare suka gama, sai hameeda itace auta." 

    *Hanna* ce tarik'e cikinta cikin muryar shagwaba tace Umma yunwa, tashi tayi taja hannun su zuwa dining, sanda sukaci suka koshi sannan suka fara tamvayar wajen anty samha. " shaida musu tayi tana d'akinta aguje sukatashi sukayi dakinta, tana waya da mijin da zata aura saiji tayi kawai anzube akanta had'eda saka ihu."

   Itama cikin razana ta saki nata ihun wanda sanda yasa abubakar dake zaune a kusa da MG yana waya saurin kawarda wayar a kunnensa, afili kuma ya furta su hameeda an isoh kenan. "

    Gaban MG ne yafadi, yanason masa tambaya amma bayaso ad'ago shi, kawai saiya share."

    Amma ransa fall yake da farinciki, ya tabbata *hannan* sa ta isoh lafiya. "

   Juyowa tayi aikuwa tana kallonsu wani sabon ihun ta dad'a sakewa sanna ta rungumesu, Umma tana daga falo amma tanajin ihunsu."

   Yan iska yaushe kuka isoh?? "

   Tun da yamma"   shine kuka shige daki? " kunsan tun yaushe nake jira kuzo kufutar da ashoben kanne yan iska kukaki zuwa."

     *Hanna* Da hameeda ne suka kalli juna harsuna hada baki wajen cewa k'anne?? "  *Hanna* ce ta tabe baki yanzu ke anty samha ku kunya bakijiba wajan cewa wai mu muyi ankon k'anne, hameeda ce ta amshe zancen haba anty yanzu dame kika fimu?" har mun daraki atsayi fa gaskiya aduba wannan zancen."

   Daura kafa daya kan daya sukayi sai wani jujjuyata sukeyi, irinna mararsa mutuncinnan. "

   Ita kuma anty samha tunda suka fara magana tasake baki kawai tana kallonsu, Ita kanta tasan gaskiya ne inba fuska aka duba ba ba'ace ta girmesu ba."

     Idan ta jiki ne ma sai ace sun girmeta. "
     Cikin rasa abin cewa tace ku6ude, _wadrope_ dina zaku kalli kalli kala biyar biyu na k'anne, uku na kawaye, green da yellow dinne na kannen saiku ebi na kawayan."

    *Hanna* ce tatashi ta bude sif din, na kawaye tafara cirowa sanda taciro set uku, sannan tajuyo, taga yanda anty tazuba mata idoh,  meye🤷‍♀?? " *Hanna* hameeda amira tafad'a  atakaice."

    Hameeda ne tataso, Itama, " na kannen ta eba set biyu."
 Kwasan kayan sukayi dasu fice, anty tatsaresu, me kuma dakuyi dana k'annen, owh anty dan munce baza musa abiki ba _doesn't mean_ ba maso, "   A'a kawai abikinne baza musaba."    suna fadin haka suka fice suka barta _totally speechless_

   Abubakar kuwa dariya yakeyi kamar dan itah aka aikoshi yi duniya."  tun lokacin bawai yakashe wayan bane, saima samusu Ita da yayi a _handsfree_ koh MG dako murmushi bawai yacika yi bane amma yau sanda yayi har hak'waransa yafito. "

   Jin muryar ta da yayi yasashi awani irin nishadi, soyayyarta ne ke ratsa duk wani gabbai najikinsa,"   wanda har wani kasala yasaukar masa dashi, " sai wani shimfid'aden murmushi wanda ke kwance a fuskarsa dayasa, kuma tunshi suka zauna a lobe wato dimfull, wanda wasu ke kira da _beauty point_."

   Damashi ko motsa bakin sa yayi, toh _side da side_ na _cheeks_ dinsa sai sun lotsa, "

   Su *Hanna*  nashiga daki duk suka zube kayan ak'asa, *Hanna* ce tacire doguwar rigar dake jikinta, da niyyar shiga wanka, yarage daga itah sai _bra_ da short din wando wanda yawuce guiwa amma baikarasa kasaba."

    Hameeda ce tashigo, daga falo taje dauko ruwan sanyi,, saurin daukan rigarata tayi da niyyar kare jiknta. "

  Wata muguwar harara da hameeda ta watsa mata da'allah banza, with dis yhur platty tommy mai mutum zai kalla?"  eh din najidai futa da'allah. "

   K'arasa shigowa tayi saikiyi kuma."

 Tsaki taja ta shige _toilet_. "

================

 Tashi yayi ya shige shaashinsa."  idanda sabo abubakar yasaba, shi bayayun sallama saidai kawai kanemeshi karasa. "girgiza kai abubakar yayi sannan shima yatashi yatafi."

  Yana shiga dakinsa wani godon alfarmane aciki, wanda daka kalla ansan gadone wanda jinin sarauta ne kawai masu irinsa wanda ake kira da _royal bed_ . "

  Farin _bed shit_  ne kall a kan gadon a shifideh, kamar yanda _paint_  nadakin yake fari,
Dakin yakai akarsa gado uku aciki kawai dan girma da kyau."

 Dakin a gyare yake tsaf-tsaf bazakace akwai mai rayuwa adakin ba tsabar yanda dakin yake so _cleanness_. " wani sanyi mai dadda dan kamshi ne ketashi wanda yahadu da kamshin _room_ _freshner_  dana turarukan dayake amfanida su yabada kamshin sanyi."

  Wata kofar _glass_ yanufa ammata _design_ mai dan karan kyau, wasu numbers yadanna kofar tabude. "

Ashe wani dakinne aciki, shima komai nadakin farii fat _pics_ din *Hanna* ne akowani lungu da sako nadakin."  tun tana karama har lokacin da tadan tasa har izuwa girmanta nayanzu. "

 Kurawa pics din idanuwa, sannan yakarasa ya6ude wata _drawer_ yadauko wani diary mai kyau harda bironsa a manne Ajiki."

  Wasu yan rubuce rubuce sannan yamayar ya aji'yeh, ya tashi zai tafi yabige _drawern_ wani file ne yafado, takardun ciki suka watse, kurawa takardun idoh yayi."

To be continued

 _Ur's_
   _z33yyb3rw3r_

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
                © _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

Page 30

*

   Tsugunnawa yayi hankali ya tarataro takardun yana me kare musu kallo. "
Afili, ya furta subhanallah wat _boders me_ Haka dahar namanta da takardunnan."

    Neman bakin gado yayi ya zauna, tabbas na gabatar da takardunnan."

   Kiran captain Ahmad yayi,"   inason ganinka yanzu, ya ajiye wayan ba'a dad'e ba kuma sai yajin ring alaman anshigo falonsa. "

     Tashi yayi ya nufi hanyar fita hadeda takardun a hannunsa, yana Futa kofan takoma tarufe, bakace dakine awajen ba saidai kayi zaton _locker_ ne haka

   Sanda yafuta adayan dakin, sannan yanufi falo."

   A tsaye ya samu captain Ahmad, yana kallonsa yayi saurin k'amewa, wata harara MG yabishi da itah. "

   Da'allah malam sauke mun hannunka, cikin gidana muke ba _barrack_ ba."  sauke hannunsa yayi hadeda dan sosa kansa. "

    Zama yayi ya nuna masa waje shima ya zauna."

  Mik'a masa takardun yayi sannan yace"  shad'af na manta dasu, karba yayi ya bude, cigaba yayi da cewa "  yaushe kaga yakamata mugabatar da su??"
  Dan idan mata ki ne ma yskamata adauka tun da dad'ewa. "

  Kallonsa yayi sannan yafara magana acikin lafazin da zaifahimceshi."

    Yalla bai da mu d'an dakatar da wannan zancen tukunna kallonsa yayi da alamun tambaya? " dalili?" yafada atakaice. "

   Dan zakudowa yayi akan kujeran, alamun yanaso zancensa yashiga."

  Yallabai kaga nan bada dade waba kaza kama ango, harara MG yasakemasa wanda bbu shiri yashiga taitayinsa. "

  Shiru yayi nadan wani lokaci." cikin hasala MG yace kaifa nake sauraro"

 Yallabai be kamata ace angabatar da wannan shaidu, batareda, kayi aureba tukunna. "

  Kasan lokaci k'alilan yarage faruwar hakan."

   Wayanna mutane ba k'ananan _criminals_ bane dasu iya _hurting_ dinta. "

   Dasuyi iya _investigation_ dan su ganota."   maiyasa kace Haka?? " meyasa ni bazasu yi _hurting_ dinaba sai itah??"

  Wani dan murmushi captain Ahmad yayi, naganin shawararsa tafara shiga."

   Yallabai _i know_ yanzuma _may be_ _they have tried several tyms to hurt_ u but Allah baibasu ikoh ba. "

   Dannasan bbu yanda za'ayi susan wyannan _evidence_ na hannunka wanda zai iya _destroying life_ dinsu kuma su zauna shiru,"   _u knw dat it can't be_. "

  Atunanin yanzu haka suna neman abinda kafiso wanda zasuyi _treating_ dinka akansa."

   Bincike bbu yanda bazai iya ba, karkasha mamakin su nemota kuma su sameta. "

   Alokacin bbu wani _sucurity_ da zasu iya kareta, amma idan tana karkashin _she will be more safe_  _than_ ace tana gidansu" .

  Yallabai idan tana karkashinka akwai * _sucurities_ masu bada duk family dinnan kariya, kuma hankalinka zai fi kwanciya da fargabar mai zasu iya aikatawa. "

   Ni yanzu aganina _is good n better_ anyi abu cikin gaggawa, ayanzu _may be they planning or up To something terrible_ wanda faruwar sa bazaiyi da'di ba."

    Captain bala da kalan kakin tawagar mu suke amfani baka ganin, wasu zasu iya binkice mai suke bi?? "

   Shiru MG yayi yana tunani dan duk maganar captain Ahmad gaskiya ne."

   Atake hankalinsa yatsahi gani yake kaman yanzuma nemanta sukeyi, atake idanunwasa suka kada sukayi red. "

   Sosai captain Ahmad yashiga rudani, yafara cewa _sir am srry i dnt meant To hurt u."_
 _No u didn't_ yafashi amsa atakaice."

   Nagode da shawarka kiramun sajen ma'arof, tashi yayi cikin 2 minute sai gashi sundawo tare. "

 Idanuwansa a lumshe dan yasan da shigowarsu."
Kaje kasamu wani Acikin soldier's d'ina, kutafi wajen captain bala, kace masa nina ce kuyi aiki tare, captain Ahmad zaimuku bayani, sannan kullum yaksance da _gun_ ajiknku, yana fadin haka ya tashi yashige daki. "

   Wajen su hanna kuwa yau kwanansu biyu da zuwa garin kano, duk yadda za'ayi event abubakar yazo sungama shiryawa biki sai k'aratowa yakeyi."

    Suna daki *hanna* na kokarin saka kaya yayinda hameeda ke zaune akan chair na dressing mirror sai kwalliya takeyi. "

  Shiri sukeyi dan zuwa wajen kai dinku nan su,

   *Hanna* Sis wai me yasa ya jalal baya fitowa ne kwana biyunna, ta6e baki hameeda tayi lokacin da take shafa, _lipgloss_
Barina je dakin sa nadu bashi tana fadin Haka tasakai tayi waje, dakin ya jalal tanufa, hameeda uwar gulma itama aguje tabita. "

  Sallama tayi amma Shiru babu amsa, kai tsaye tasakai ta shige,"

   Ganinsa tayi yayi rigin gine, yayi zurfi atunani, Zama tayi a bed side drawer amma baimasan da shigowarta ba, aranta tace su yaya anfad'a fahh, dan wannan tunanin sai wanda ya nutsa kogin soyayya. "

  Ya jalal!"  ya jalal " takarkarewa tayi ta kwala ihunda yasashi mikewa zaune bbu shiri,
Kada kai tayi sannan yafara rero waka."

    🎼Alamar tambaya tanaga mai yawaita tunani 🎼🎼musamman yashiga halin soyayyar zamani🎼🎼yau gashi ciknta 🎼🎼yarasa wanda zai fiddashi 🎼🎼sai ita masoyiyarsa wanda sukayi kyau da kamanni🎼🎼

   Kallon mamki kawai yatsaya yana mata, bai k'ara sarewa ba Sanda yaji hameeda tashigo tana nata wakar. "

   🎼abinda yake ranka zaka fitar ka huce tunani🎼soyyace aranka🎼garaka fada bazata ficeba🎼🎼

  Tunani yafara aransa, kaddai yarannan sun fahinci yana son *hanna* ne

  *Hanna* ce takatse masa tunaninsa, ta6ashi tayi yajuyo gira daya tad'aga masa wacece? "

  Kece yace" zaro kwala kwalan idanta tayi " saurin gyara zancen yayi Kece fitinanniyar dakika katseni daga tunaninta ai."  sauke ajiyan zuciya sukayi daga itah har hameedan, toh yaya wacece? "

 Katse zancen yayi kutashiku fita kubarmin daki, Haka dole ya korasu."

  Maya fansu suka dauko suka fita dan kai dinki. "

 Duk wani abinda ammahtasan zai kawowa amma kudi sanda tad'aga tasayar, yanzu Haka tagama hada kudin zuwa gobe dasuje gun malam."

 Hanna sunfito daga gidan anty hindatu, kasncewar anguwar bame jama'a bane yasa titin bbu kowa. "

  Kaitsaye suka nufi titin dan tsallake shi, a lokacin motocin MG suka danno hancinsu atitin."

To be continued

 _Ur's_
    _Z33yyb3rw3r_

[12/2, 9:26 AM] Anty Jamila D Ili: *BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )


My first novel

_Wannan fage din nakune masoyana *maman zarah 😍* *murjanatu(admin)*
And *zuwairat(addansumy)* zaynab bawa na kaunarku kamar yadda kuke kaunarta *ILYSM*_


Page 31



*
  Titin sukaje tsallake wa a lokacin  motocin MG suka danno hancin motarsu Titin dake layin. "


   *Hanna* ce ta juya da sauri sis na manta phone dina Adakin anty bari nadauko,"   sai kin dawo amma nikam barin tsallaka zan jiraki. "  juyawa tayi da niyarr komawa ihun da hameeda ta sakene yasata juyowa da sauri, ganin hameeda tayii akasa, ashe lokacin da tajuya take yiwa Hanna magana a lokacin motocin sun rigada sun zo tsakiyar titin, hameeda bata luraba ta shiga sukuma basu tsaya ba sukaje gadan gadan kanta," aikuma kunsan base nafada ba kunsan sojojin bazasu tsaya danta tsallaka ba. "


   Aikuwa hakan ya bala'in 6ata ran Hanna ganin ko tsayawa basuyiba dan duba lafiyarta, afusace ta dauki wani katoton dutse, dan niyar jifan motocin, hanata hameeda takeyi amma fir taki jefa dutsen tayi Aikuwa kamar ta saita sai motar da MG yake ciki."

   K'aran dutsenne yadawo da hankalin MG dayake Waya, lokaci daya hankalin sojojin duk yatashi. "dan sun d'auka hari aka kawo musu, MG ne ya umarci a tsaida mota, ganin fuskar da yafiso aduk duniya idan aka cire na mahaifansa, ta madubi sai huci takeyi."


    Ganin antsaida motane yasa sojojin fir fi towa kowa da bindigarsa a hannu suka zagaye motar da MG Ke ciki. "


   Umarta yayi da abude masa kofa babu musu suka bude, captain Ahmad dake gaban motanne yafitoh yana tambaya ina zaije amma ko kulashi baiyiba ya nufi wajan su *hanna* su sajen ma'aroof da motar su kecan gaba suna gadin *hanna* suma ganin haka yasa suka futo, suka nufi ogannasu. "


   Su captain bala ma da suke can baya wanda dama sunga wucewar ogannasu amma ganin ya tsaya suka fito suka nufesu, hangosu yayi daga nesa ya musu alama dasu juya, bbu musu suka koma, ya karasa wajenesu *hanna* datake rikeda kafan hameeda tana mata sannu. "


 Hameeda ce tafara kallonsu, ahankali tabugi *Hanna*  tanuna mata ai suna kallonsu atake suka mike tsaye cikin su yahau lugude."


    Yana karasowa gabanta yafadi, subhanallah yahadu Addu'oi kawai takeyi dan azatonsu gamo sukayi deyi wuya samun namiji mai kyansa, hameeda kanma dabadan kartayi karyaba datace har daukan idoh yakeyi, "

   Ta6a Hanna tayi kinga abinda kikaja mana ko" kin ta6o mana dan balarabe. " yana karatosu wani ni'imtaccen kamshi na ziyartarsu"  dakyar *Hanna*  tattaro kuzarinta cikin jarumta dan kwarjini gareshi kamar zaki, duk sai taji yacika mata idanuwa idanuwa, adan zafafe tace. "


   Tsayawa kazo yi ko kazo bata hakuri ne?? Shiru yayi ya tsaya kallonta, Eyhem tambayan ka nakeyi kawani tsareni da idoh"  azafafe wani soldier yayi kanta da niyyar marinta, captain Ahmad ne yayi saurin tsareshi, katsira da aikinka kawai yafada masa. "

    Rike k'ugu tayi tana karar raya, sannan taciga ba dacewa" ai dama nasan irinku bakusan darajar dan adam ba burinku kawai kuci mutuncin kowa." kokadan baiji zafin magan ganinta ba saima wani sanyi dayake ziyartar zuciyarsa, gawani irin girma kyau da cika idoh datayi masa, wutar santa ne take kara ruruwa acikin zuciyarsa. "


  Hameeda ce take ta ta6a ta akan tabari amma ture hannunta kawai takeyi."

  Wasu daga cikn sojojin ne sukayi kanta a hasale, daga musu hannu yayi alamun su koma Haka suka koma badan ransu yasoba saiwani huci sukeyi, araina nace yanzu yanda kuke zabga-zabga dinnan idan aka barku saiku daketa? "🤔. "

   Karasawa yayi har gabanta alokacin sai faduwa gabanta yakeyi, gawani irin kamshi dayake shirin rikitata ." yatsunsa guda biyu yasa ya 6alle mata baki ai babu shiri tasaki ihun azaba, sannan yace" bbu kyau yin rashin kunya anah gaba dakai" yafad'a kamar mai yin rad'a, aikuwa tana sakee bakin tace Allah ya'isa na mugu azzalumi. "
aibaisan lokacin dayawaro idanuwansa ba, wato ita wannan yarinyar batada tsorone ko kad'an?" aikuwa bata ankaraba ya k'ara 6alle mata bakin, nanma tasake sa wani ihun Atake kuma tace Allah ya'isana, aibata k'arasaba yakara 6alle mata baki,"

  Ihu tasa wannan karan kan harda bubbuga k'afa takusan  sa MG dariya dakyar ya danne," Allah yahhh, aibashiri tasa tafukan hannunta tarufe bakin,"

 D'an sunkowa yayi yace Allah yayime? "wata uwar harara da doka masa," haderai yayi yace, idan kika k'ara yiwa wani rashin kunya nidake, yafada had'eda nuna kansa da ita wanda inba ita data ganiba bbu wanda yafahimta."

  Yana juya baya tace kuma sai Allah yasakamun, a hankali kaman mai tsoron yajita, aikuwa karaf a kunnensa juyawo yakara yi atsorace tayi baya, dakatar da ita yayi sannan yamatso yanda bbu wanda zaijishi, yace idan kikayi hakuri kwannan ma zaki rama da kanki, yana fadin Haka yajuya yabarta adaskare agun takasa gane wannan maganarsa ta karshe. "


   Juyawa yayi wajen hameeda, sake fuska yayi, yayi wani _killer smile_ yamata wanda yasa hameeda sake baki kamar wata doluwa."

    Cikin kwantar da murya yace _sorry_ _dear_ bansan haka zaifaru ba kiyi hakuri. "

   Hadiye wani miyau tayi bakinta har yana 6ari tace bbu" ""babu komai. "  wata 'yar dariya yayi, ok ko zaki shigo musaukeki?"

   Wani bakin ciki ne ya turnuke *hanna* ganin yanda hameeda ke binsa da ido kamar sokuwa. " haka kawai ta tsinci kanta da jin haushinsu duka, fuuu tabar musu wajan tayi ta nufi gidan anty hindatu."


   Kallo suka bita dashi, sannan yadawo da kallonsa kan ta, muje ko yace mata, kallonsa sa tayi sannan tace, idan na tafi bazataji d'ad'iva kuma kaga ita bakuwa ce batasan gari bah. " tafad'a irin bahaka taso dinnan ba."


     Karki damu, kije ki kwantar mata da hankali naga kaman ranta yabaci karki barta cikin bacin rai."

  Kallo mamaki tatsaya yimasa, kanne mata ido daya yayi sannan yajuya, ya nufi motarsa, captain Ahmad yagani sai wani rike dariya yakeyi, harara ya 6alla masa. "

   Kai tsaye mota yawuce, suka rufa masa baya suka tafi."

   Duk abinda malam yabukata Ammah ta shirya Kai tsaye suka Kai masa, ya umurcesu dasu dawo gobe. "

   Kaitsaye washe gari sassafe suka wuce ya shaida musu cewa komai ya wakana amma bazaiciba harsai randa hanna suka had'u da najeeb."

   Abinda Ammah tamanta shine tacewa malam ya rabata da najeeb amma batace masa ya rabata da kowani saurayi ba. "



  Yaune ranarda su chief suka yanke danyin meeting akan MG, suntaru awani office wanda duk kujerune anzagaye da kujeru, zama sukayi sukafara gudanarda abunda yakawo su."



To be continued


 _Ur's_
      _Z33YYB3RW3R_
[12/2, 9:27 AM] Anty Jamila D Ili: *BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

My first novel

 

Page 32





*

  Tana shiga da gudu takarasa kamar wanda aka jefota, atsorace anty hindatu tatashi tana tambayarta maiyafaru amma ko kulata batayiba, tashige daki ta fad'i rub akan gado tafashe da wani irin kuka maicin rai. "

   Tunda take arayuwarta bbu wanda yataba mata cin mutumci irin wannan _he just ambarass her  in public_ agaban jama'a atake wani irin tsanarsa da baibayeta zuciyarta jitayi batada wani mak'iyi kamarsa wani irin * _hatered_  takeji wanda bata tabayiwa kowaba."

   Ringing da wayar ta tafara akan dressing mirror ne yakatseta, da kaman bazata dauka ba sai wata zuciyar tace mata ko najeeb ne, dan ita yanzu abin najeeb har mamaki yake bata. "  saiyayi 2days  bai kirata ba kuma some tyms kota kira baya picking."


  Wiping din tear's nata tayi tanufi kan dressing mirror ta dauki wayar,  To her biggest suprise sai taga amirace ke kiranta, with full of happiness tayi picking, beb u just foget about me, badai kunkamo hanya ba?? "  nop bamu kamo ba, but wen dear??" is only 2days yayi remainig afara event fahh, " srry To say dat but beb inaga zuwannawa ma zaiyi wuya, "  dan dady ya han,,, ai bata bari tagama ba tayi hanging call din, sosai ranta ya6aci, wani irin bakin ciki ne ya turnuk'eta she feell much more anger than abunda aka mata recently."

 Anty hindatu na falo gabaki daya she worried batasan maiyasamu sister dinta ba, jiran shigowan hameeda kawai takeyi. "

   Can kuwa sai ga hameeda, dasauri anty ta taryeta, hameeda wat happen To dis stubborn naga ranta abace."

  Is nothing fa anty, kawai mun d'an haura ne, " wani tsaki anty taja mtsww, wawiya shine da d'agamin hankali, tana fadin haka tanufi daki."

  D'aga cutton din dakin tayi, da'alla wawiya zoki fucemin agida, azuciye *hanna*  ta d'ago da'alla awani gidankin da ko kyau bbu, eh naji dai. "

   Suran phone dinta tayi, sanda tazo dai-dai ita, wani dirty look da wurga mata sannan tace idanni ne Wallhy saikinzo neman, with dis ur crumpy leg's, duka takai mata tayi saurin go cewa"  kiyi ki fad'i akan wannan katon ciki naki ki haifi dan wata takwas bbu ruwani danni gida zanwuce,  eh toh banza inaruwanki, tafita tana mita tsafar rowa sai kuyi gida 2 bed rooms dan karkowa yazo ba, dama haka halin anty hindatu da *hanna*  saidai basu haduba sai anhaura amma na'yan minute suka rabu kowa yafara missing dan uwansa."
Dama haka mabiyi da mabiyi suke dan *hanna*  ita takebin hindatu kuma tsakaninsu ratan 1 and half year ne shiyasa suka taso kamar sa'anni dan *hanna* gani takeyi kamar rana daya aka haifesu. "


    Hameeda ta tarar a falo tana jiranta, wuceta tayi kaman bata ganta ba dan wani irin haushinta takeji."

   Binta hameeda tayi tana bata hakuri dan gaskiya she feells very bad ace wajen nema mata 'yanci an 6ata ran' y'ar uwarta. "

   Dakyar *hanna*  tasauko maimakon suyi gida sai suka wuce yawo, sai closed to magrib, suka nufi gida."


   Mota suka kalla afake, cikn sauri suka karasa dan haka ya nuna musu mama ta isoh, ciki suka shiga da gudu suka fad'a kan mama ai ba shiri tafara turesu da'alla kutshi karku karyani."
 *Hanna* ce tatashi abinda cinyar kinma bawani dad'i na Umma yafi, tana fadin Haka tatashi tayi daki, hameeda ce tabita da gudu zata daketa, itama gudun tasa sukayi daki ganin mutum akwance akan bed dinsune yasasu tsayawa cirko cirko."

  Hameeda ce takarasa ai ```to her biggest suprise``` amira ce akwance akan bed d'in tai saurin d'ale gadon tana ihu ta bata wani, ```huge hug``` ai *hanna* na ganin haka itama tayi ```landing```akan bed din tayi hugging nasu duka sanda suka ciki gidan da. ```Screaming``` dakyar suka ```letting go``` na ```hug``` din *hannace* tace ```OMG beb u suprise us``` i knw shine dazu hadda hanging dinmun call ai, srry beb kinban haushi ne shiyasa, to ba ganiba, sai abude chapter  na rashin mutumci," hameeda tace nikam book guda zanbude ba chapter ba, dariya duka sukasa, hameeda ce ta k'ara cewa ke beb bakisan mai yafaru recently da wannan beb dinba, *hanna*  ce tayi doka mata harara kinga bansan iskanci Wallhy, leave her beb nidai kawai bani nasha, haka hameeda tayita koro mata labari, ai dan dariya amira har riqe ciki takeyi, da'alla banza ```stop lough ding at me``` dakyar ta tsagaita wallahy kalan luv dinku ne so muaahh 💋, banza baki ganshi bane wannan dan ego din,"
 uhm dama ki fad'i gaskiya amira tace. "

Can kuma kaman wanda aka soka mata allura tace"  hameeda baki noticing ba lips dinshi is like yana shafa janbaki, amirace tayi saurin cewa anzo gun, dai-dai gunma kuwa inji hameeda, shiru tayi musu kawai, amira ce takara cewa beb dont tell me dat his lips are so lucious?"
Banza tayaya zansani,
```oh i see🤔 but I definitely knws dat u feell like kissing him dat tym```iya k'ulewa *hanna*  tak'ule, she feells kaman ta aikasu lahira,
anahaka hameeda takara cewa watoo dama yana magana ke lips dinshi kika tsaya kalla ta fad'a, ```oh ya rabb🤦‍♀ am leaving dis room right now``` tana fadin haka tatashi tafuta had'eda banko musu kofa, hameeda ce tadaga murya yanda zata jita tace tasbahy alah khair habibty, dantasan abu mai wuyane tadawo dakin. "

  Direct dakin da aka killace anty samha danyimata gyaran amare ta nufa."  tanashiga shiga tasamu anmulke ta da kayan gyara kala kala. " zaunawa tayi itama tace sai 'anyi mata Ahaka Matar tazauna itama ta mulketa tsaff."   dan ita aganinta kudintane zaikaru bbu ha'incii tamulketa kamar yadda tamulke samha haka itama tamata. "

   Umma ce tashigo hannunta rikeda abu a kofi."  tayi mamakin ganin *_hanna_* amma saita share, ganin *hanna*  amulke take dariya takamata aikuwa tahau yinta bakakkauta, turobaki tayi Umma menayi kikemun dariya? "
 srry My doughter mikawa anty samha kofin hannunta tayi, cikn nuna kyama samha takarba takafa kai, tafarasha, ganin tana shirin shanyewa yasa *hanna* tayi saurin faucewa."

  Wani discusting look anty samha tabita dashi, Umma kuwa tatsaya kallon ikon Allah." turo baki tayi yanzu anty inwajen saiki shanye? " tana fadin haka batajira amsaba takafakai, aibashiri zata dawo dashi, Umma ce tqkatseta, Wallhy ```if u dare```  saina ebo wanda yafishi  ```an then feed u like a baby``` bashiri ta shanye tasss."

  Blanket taja tarufe su sannan tafita, anty samha ne ta juyo sukayi facing each other, habibty, Yes aunt, who's the luckiest guy?? "
Hmm"
Why humming dear?" "tell me."
Hawayene yafara sintiri a fuskanta, oh god dear, a ranta tace sumtin is behind that tearness,
Tashi tayi tazauna itama ta tayarda itah. "
D'ago fuskanta tayi, habibty tell me whats wrong?".

Ai kaman jira takeyi tafada jikinta tafashe da kuka." plz habibty stop crying and tell me whats wrong?? "
 Rarrashinta tayi tayi Ahaka hartayi shiru ta, zayyane mata everything, sanda tayi kwalla dan tausayin kanwarta da tsanar hali irinna Ammah. "

Cikin kuka tacigaba da cewa"  aunt i love him i dont wanna loose him, he's all i got and i want, he's driving me crazy aunt,"  am dying without him, saurin rufe mata baki tayi,shhhh stop saying those horrible things dear, yaushema kika sanshi just afew months back, har daza kiyi tunani bazaki iya rayuwa babu shiba," u had to be strong my dear, ".    try hard to show him u can live without him either kinji dear?" Daga mata kai kawi tayi."

   Haka tayita rarrshinta hartayi bacci.".  Tadaura niyyar saita cire mata najeeb arayi. "
Ita hankalinta yafi karkata da masu binta, Dan tanagani kamar wanine yake dakon Santa kuma bazata bari wani najeeb lokaci daya ya masa shigan sauri ba. "

  Araina nace kaji Mata saikace Wanda takeda tabbacin hakan🤔🤔 ahaka bacci ya kwashesu."





Read more😜



To be continued


Ur's
       z33yyb3rw3r
[12/2, 9:29 AM] Anty Jamila D Ili: *BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

My first novel



Page 33



*
  Sai wajen three 3:00 am suka farka."
Matan dake dama already agidan take har tazo dan itama ta tashesu. "
 Warm water tafara hadawa samha ruwan yasha different types na turaruka, wanka taje tayi, sai bayan tafito ta had'awa *hanna*  wankan itama tayi,"  tun a toilet din take kallon skin dinta, yayi wani soft an silk, sai sheki takeyi yadda kasan skin din nicky minaj. "
  After she come's out ba anty samha bama har  maigyaran sanda tatsaya kallon ta."  tanada irin oily skinny ne mai shegen daukan gyara, anty samha ne tahad'e hanna yenta👌 looking gogeous 😍my dear, " wani dan rangwada tayi had'eda farfari da idoh sanna tace tanks aunt😘."

Kallonta anty samha tacigaba dayi, habibty baki ganji bane harzaki tsaya yin kuka akan wani najeeb, aikin wucewa nan."
U alway's look more beautifull My dear. "
 *Hanna* ce tace, anty toh idan wani aiki ne yake keeping dinsa busy fa??"  karnayi saurin yanke decision  da zanyi regretting, at the end. "
Juyo da ita tayi suna fuskantar juna, sannan tad'an tallafo face nata tace," no  My dear" if he really care's he will always find a chance. "
Is not fair been busy to the one's we love?" kwace fuskanta tayi ganin haikan tadage so take ta rabata da masoyinta. "

 Cut the crap aunt, i knw sumthin Is behind, and i won't let U to ruin my relationahip, no matter how couse." kallon mamaki damata tarasa wacce irin yarinya ce, saikace wanda yamata black magic. "   ita kwata kwata bai kwanta mata ba, bazata lamunci," yaringa sa mata yar uwa cikin tashi hankali ba. "

  Habibty kinaga kaman inason rabaki dashi ne, amma Allah yamana za6i," amin tace. "

  Anty kinsan maiya faru jiya?" nop my dear saikin fada "
Kowani tunani tayi kuma saitace, just foget it,  Kallonta tayi maiyasa zanbari fadamin kawai, nop anty ki mance kawai,"  Allah yashiryeki kawai anty tace, ita kuma ta amsa mata da ameen. "

 

Mayukan da anty samha take shafawa itama ta mulke jikinta dashi."
Dama already tayi alwala, sallah tagabatar, sannan takoma bacci bata tashiba saikusan 9:00 . "

  Fita tayi zuwa falo, ganinsu mama azaune da sauran 'yan uwa yasata gaishesu."  sannan tashige side din dasu hameeda suke."
  Shiga tayi bbu wacce takula aciknsu tanufi inda tabar phone dinta. "
  Dauka tayi tazauna tana danne danne, jira takeyi sumata magana amma bbu wanda yakulata."
Wani bakin ciki ne yatokareta, tashi tayi taje gabansu, beb baku kalli yadda skin dina yayi bane, "
Nunawa sukayi basusan tanan ba."
Bebs am talking,
Ainanma ko susan tanayi, Bebs are you deep? "
Ganin bbu me kulata ne yasa tayi hanyan Fita azuciye."
Dariya suka fashe da ita sannan suka tafa. "
Bakin ciki yasata banko musu kofa."
Tayi dakiin yaya jalal. "

================

Zaune suke awajan  meeting din kowa ya hallara." juayawa yayi ya kalli wani mutum da fuskar sa ko kyan kallo bbu. "
 Ka nemomin tarihinsa kamar yadda na bukata??  Eh nasamo,"  Ka tabbata baka fidda ko mutum d'aya ba aciki? "  eh"   toh, lets  watch. "  video din sukayi playing."
Anyi sa'a ansamu tun farkon fitowar *hanna*  daga gidan maman amal, harkarshe. "

  Kashe video din sukayi,"   daya daga cikinsu ne yafara magana, gaskiya wannan ba setup bane kamar yadda muke tunani, "
Dole yanada wata alaqa da wannan yarinyar."
Fadowa kawai yayi akan d'anka,"
  Amma kuma hakan bawai yana nufin ya kyalemu bane, dole mudauki mataki tun kafin ya waiwayemu. "

  sadam""  yes sir ",   inason yanzu katashi kabamu labarinta duk wani abinda yasha feshi."



To be continued



Ur's
    Z33yyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
                © _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

My first novel



Page 34



*
 Dakin yaya jalal tanufa, dirct, knocking kofan tayi, shiru akayi can takara, yaya is mee
Shiru nanma ganin haka yatabbatar mata yabayan juyawa tayi ta nufi dakin anty samha. "

  Shiga tayi tasamu anty samha sai waya takeyi batasanma tashigo ba, sai wani Kashe murya takeyi, biten din lower lips dinta tayi, sannan tayi shaking head dinta, arqnta tace, u always trying 2 seprate me from My very own, amma ke kinwani zage sai shan soyayyarki kikeyi, daki gane tafada, sannan tayi kwafa. "
Gefenta taje ta zauna, chicks dinta ta tallafe da hannunwanta takura mata ido, dan d'aga wayar tayi akunnenta, d'aga mata gira d'aya tayi sannan tayi lowering  voice dinta tace,"   what happen dear?"
Shaking kanta tayi sannan tace bbu komai,"  ok why d look?, "
Kawai kunbirgenine, 👌 mayar wayan kunnenta tayi sannan tacigaba da phn dinta."
Kamar wanda aka cikareta tace, anty da alama kinasonsa dayawa? "
Shiru anty tayi for a while, sannan tamasa sallama juyawa tayi, tayi facing nata."
Magana tacigaba, anty baki ta6a tunani kamar yadda kikeson yaaa abubakar, haka nekeson najeeb ba. "
May be ma irinsonda nake masa yafi wanda kika yimasa."
Wani irin tausayin *hanna*  ne yakamata, a hankali tace iknw how u feel dear, but yakamata koyaya destiny dinki yazo kikarbeshi hannu bibbiyu, sai kikalla Allah yasaukaka miki. "
Ahaka tayita rarrashinta har yamma suna daki suna tad'ii da anty samha batakarabi takan su amira ba."


 Najeeb na zaune adakin sa, tunani yakeyi yau kusan satii d'aya da yiwa abbansa magana, amma Shiru haryanzu, be nemeshiba, kuma bai bashi wata kwakkwaran evidence nakin zuwa nema masa aure ba."
Gashi yarasa meyake damunsa ko waya ya dauka zaikira *hanna*  sai yarasa dalilin sa zai hanashi."
   Wani iri yakeji wanda idan bai ganta acikin wannan week dinba sai ahankalii. "
Yanke shawara yayi kawai zuwa nanda 2days zaije kano, dama already yasan address din."


 

  Umurtar sadam yayi daya tashi ya basu labarin MG. "
```Wai shin waye wannan MG d'inne daya addabemu kam??```


       *WAYE MG*

Abdullahi Abudulaziz lamido ne asalin sunansa."  asalin yan garin kano ne, masarutar kano."
Kakansa shine sarkin kano mai rasuwa. "
Abdullahi muhammad lamido, yanada yara shida,"
Abudulaziz shine babban d'ansa sai abudulrahman sai khadija da kuma halilullahi, sai hannatu da kuma autarsu sa'adatu. "
Shekaran babansu talatin akan mulki Allah yamasa rasuwa, alokacinne Gashi babban d'ansa baiyi aure ba."
 Shine aka samu yar gidan k'aninsa mahaifinsa wanda yariga mahaifin nasa rasuwa. "
Aka daura musu aure badan yana sonta ba."
Sannan aka damka masa sarautar k'asar kano. "
Mutane sunajin dad'in mulkinsa dan halinsa d'aya sak da mahaifinsa."
Talakwa kai hadda ma masu kud'i suna yabawa kwazonsa. "
  Shekararsu d'aya da aure Allah ya azurtasu da yaro namiji, asaka masa isma'il sunan mahaifin kilishi, sosai yaron yariga ran mutane, magajin sarki."
Iya gata yarima isma'il naganin gata sosai. "
Alokacin tanada cikin secound born d'inne yad'auk'eta, zuwa dubai (abu dhabi) danyin shopping."
  Wani tamfasetsen shago sukaje dake cikin marina mall (abu dhabi) . "
Shagon duk kasuwar yafisu girma, kowani kalan zinare kakeso awannen shagon daka sameta, duk prize dinsa."
Nufan shagon sukayi dan sayan zinare, bayan sunshiga, ne kilishi tafara za6a. " alokacin wata yar yarinya tashigo, wanda asa'anni zata Iya kaiwa kilishi, dan auren wuri akayiwa kilishi tuntana 15, gashi yanzu almost 3yrs da aurensu."
Kallon yarinyar yatsayayi dan lokaci d'aya yaji yakamu da sonta luv at first side. "
Hartagama abinda zatayi tafice, dawayo yabi bayanta, yaje yasameta, bata nuna kyankyaminsa nakasancewa bakar fata ba."
Kwatancen gidan su tamasa be dauki lokaciba yaje dafarko iyayenta sunki yarda, hqr takaiga kullum, yana kofar gidan amma bbu mai kulashi. "

Ita kuma Allah yadaura mata sonsa sosai, yadda kullum cikin kuka take."
Takurin daya ke musu ne yasa suka yanke shawarar bashi amma sai sunyi bincike. "
Binciken da sukayi ne ya nuna musu matsayinsa bakaramin mamaki sukayi na ganinsa babban mutum amma yake irin kwantar dakaiba."
Dan mahaifinta yasan kasar kano kuma yasan irin mutanen dake cikinta. "
Amma ace wanda yake mulkarsune ya kwantar dakai wajn neman auren 'yarsa."
Haka akaturo magabata aka gama komai. " kilishi
Bakaramin tashin hankali ta shigaba da wannan zance."
Sanin bawani sonta yakeyiba yanzu kuma yasamu wacce yakeso, kuma balarabia. "
Da zigin mahaifiyarta suka fara shiga bokaye da sunan malamai amma bbu abinda yafasu dan aurekam sanda akayishi." sai bayan aurnne yasan cewa wannan shagon daya ganta ashe shagon mahaifinta ne, sosai yake iya gwargwado na nuna adalci atsakaninsu. "
Amma duk da haka kilishi tananan da kishinta, saidai kokad'an batada bakar zuciyarda zata cutarda raheema (ummii)."
Hakadai zamnnasu yake ita bawani shiri sukayi ba amma kuma ba fad'a ba. "
 Bayan auren da wata biyu da koma Dubai dan k'arasa karatun ta."
Tafiyanta ta da d'an wata hudu kilishi ta haihu ta haifi mace, yamayar mata da sunan kanwarsa khadija. "
Ummii tazo suna, gama ta arkizi ta had'o mata dan harda zinare."
Lokacin ita kuma cikinta na kinamin wata biyar. "
Ganin cikin baid'agawa kilishi hankali ba dan tasan ko yanzu itace da gida."
Bayan wata hud'u tagama karatunta. "
Ak'asar haihuwa ta sameta."  anan ta haiho danta namiji kyakkyawan gaske. "
Kafin suna suka dawo Nigeria."
Asuna yaro yaci sunan kakansa Abudullahi. "
Iya buduri anyishi,
Wanda kowa mamakin hakan yakeyi dan ko sunan isma'il yareema, ba'ayi buduri haka ba."
Aikuwa yaron yashiga ran fulani, mahaifiyar mai martaba. "
Kullum yaron yana wajanta, hakan kuwa bakaramin k'ona ran kilishi yayiba,"
Wajen mahaifiyar ta taje ta shaida mata da kuka. "
Ran mahaifiyar ta yabaci tana ganii ga wanda yafito d'an dangi nan sai wani bare zataso."
Bayadda basuyi naraba shi da itaba amma abu yaci tura haka dai aikinsu baiyiba su kuma basu hakura ba. "
Yafara girman a kullum kyawunsa ne yake dad'a fitowa."
  Yanad'an shekara shida aka daukeshi zuwa makaranta a russia. "
Fulani kuka tayi tayi akan baza'a kaimata jika kasar arna ba amma haka bayadda ta'iya, haka Ummii ba bawai taso bane."
Kowani bawan Allah yaji wannan abu saiya tsaya jimami ace yaro tunyana karami da'a daukeshi zuwa wata makaranta. "
Haka dai aka tafi dashi bawai danran kowa yasoba, abinda yad'an  ragewa Ummii zafi dalilin lokacin ta haifi afeeya."







Sai bayan shekara shidda, kafin yake dawowa hutu, sai dai iyayenshi suna zuwa wajenshi, makarntar ta sojoji ne tun suna k'anana ake kaisu, yakanyi wuya asamu wanda ya fara tundaka farko har ya gama." wasu idan suntafi hutu basa ta6a dawowa, wasu kuma yawanci da girman su suke zuwa ba rainon makarntar bane,
duk hutunda yazo yakanyi 5-6 month kafin yakoma. "
Shekara shidan farko yadawo yasamu labarin mutuwar yayansa, yareema isma'ill sakamakon hatsarin mota."
Sosai mutuwar tashigi 'yan gidan dan yafara girman yakai kusan 16yrs lokacin. "
Shima mutuwar ta shigeshi sosai dan Kowani zuwanda za' ayi masa tareda yayansa ake zuwa."
Daga nan kuma duk wani soyayya ta tattaro tadawo kansa. "






  Shekaransa 18 a makarantar alokacin yagama inda duk yanda sadauki da jarumta takai to yakai, masu karatu basaina tsaya yimuku vayani ba kunsan yanda sojojin rusia suke duk duniya bbu sojojin da suka kaisu horuwa, kuyi imagine wanda yayi shekara 18 yana horuwa akasar."
Duk ciki su uku ne suka fita shine wanda yazo nafaarko. "
Dan tunda suke ba'atabayin jarumin d'alibi kamarsa ba."
Hakanne da suka gani sun tabbatar idan yatafi k'asarsa  wannan horo dasuka masa yatashi abanza. "
Ganin Hakanne yasa suka ce sudasu rikeshi."
Aranda akazo passing out dinsu ne, alokacin duk wani family dinsa sun hallara. "
Mamaki ne yacika mutanen gani duk bak'ak'en fata ne danginsa."
Sunga su kansu ma yafisu kyau. "
Duk wanda akagani awajen taron har inde daga family din MG yafito to karramawarsu dabannee."
Kowa nema yake ya gaisa dashi ko family dinshi,
Duk wani kyauta shiyasamesu,
Inda kasashe da dama suka bid'ar yamusu aiki. "
Ganin Kowani kasa na bukatarsa yasa, kowacce tasa hanu aka bugamar starm na sojan k'asa da k'asa."
Haka taron ya watse kowa na farinciki,
Barin family na MG dasukejin kansu asama. "
Tunda intisar tad'aura ido akansa, taji tanasonsa, dafarko yad'an fara kulata, amma tunda yayi wata yafiya yadawo yabirkicewa kowa dan ko kallon arziki bata samu."


Sadam ne yad'an nisa sannan yace "
Ayanzu haka labarin da nake baku, yaran mahaifinsu shida, khadija, abudullahi (MG), afeeya, affan halima da labba.

Sannan ya nisa yace wannane takaiceccen tarihinsa."
Daya daga cikinsu ne yace, amma duk wani pics da labarin bbu hoton wannan yarinyar aciki. "
Me hakan yake nufi kenan?"
Ita wacece idan ba daga cikin family dinsa takeba? "
Dayanne yace tabbas tana da mahimmanci awajensa, dan wayanna sojojinsa ne."
Sadam ne ya nisa sannan yace, tabbas dan alabarinda muka samo mungano tun shekarar daya dawo biyu daga cikin sojojin sa are missing kuma haryau bbu wanda yasan yanda suke. "

Nisawa yayi sannan yace toh kanemo mana ita wannan yarinyar wacece?".



To be continued


Ur's
     _Z33yyb3rwr3r_

[12/2, 9:28 AM] Anty Jamila D Ili: *BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

My first novel



Page 35





*
   Ahaka suka k'are meeting d'in, akan za'a nemo musu wacece ita?"  kuma menene alaqarsu da ita? "


   Haka yau takasance ma, agun anty samha ta kwana, su amira sun bata hakuri amma kaman bada ita sukeyi ba."
Haka yau ma takara mulke jikinta da had'i, sannan suka kwanta. "
Amma kokadan bata bawa anty samha kofar da zata mata maganar najeeb ba. "
Dasafe kuwa wani irin kyau tayi fiyeda najiya, kuma yau takasance ranar da za'afara event. "
Mama kasa hakuri tayi sanda ta tanka." ke wai mai kika fara shafawane kam?"
Turo bakinta tayi, "
Zaki fad'amun ko saina bige wannan bakinkin?"
K'in mayarda bakin tayi tak'ara turoshi, "
Tashi tayi da niyar bigeta, ganin haka yasa takwala ihu."
Aikuwa dama umma nawajen, "
Tashi d'aya tafara tahaukan Mama ta masifa,"
Ke banasan shashanci kina jina ko? "
Ina ruwanki da kalar da tafanta tayi?"
Hava yaya kikalleta fa sai kace wata mai bleaching ki kalla yadda fatarta tayi haske? "
Umma ce" tace yanzu ke aisha haryanzunki bazaki iya, bambamce farin bleaching, dana gyara ba? "
Toh tare ake musu gyara itada samha."
Jin hakane yasa hanklain Mama kwanciya,"
Hmm kawai Mama tace daganan bata sake cewa komai ba. "
Shiga d'akin su amira tayi, duk d'insu sakewa sukayi kamar wanda bbu wani abu dan sukansu fushin da sukayi kowa yaji jiki, hira sukeyi sosai, can wayar ta tafara ringing ganin anty samha ce mai kiran yasata saurin amsawa."
Hellow" anty, "
Kuzo d'akina kedasu amira, bbu 6ata lokaci ta shaida musu kiranna anty samha Tashi sukayi suka nufi d'akinta."
Shiga suka yi tana kan gado. "
Dawasu kaya awajenta."
Zama sukayi, harhad'a kayan tayi awata jaka mai kyau sannan ta d'ago ta dubesu, mikawa *hanna*  jakar tayi, gashi dan Allah yanzu kukai fadah,  fad'a baki sukeyi dukkansu suka ambaci fadahh?"
Eh " kanwar sace yar gidan sarki tadawo daga school kuma duk wani ankonta awajena yake, kunsan zuwa jimawa zata buk'ace su."
Ta6e baki amira tayi to ai anty sai abawa driver yakai mata danni wallhy bansan rainii takareshe maganar tana kawarda kanta gefe,"
 *Hanna*  kan wayarta tafara dannawa dan tasan wannan zancen bamai yiwuwa bane."
To ke anty ita baza tazo ta kar6a da kanta bane? "
Ko tsabar sarautar ne sai ankai mata?"
Dan Allah ni basaina tsaya magana ba idanna isa daku kukai mata. "
Idan kuma bazaukai ba shikenan."
Dan akwai abunda zata baku kuzomin dashi ne. "
Haka badan ransu yasoba suka tashi danzuwa kaimata,
Kuma abinda yafi ci musu raima shine wai ba driver bane zai kaisu a taxi zasuhau futa sukayi kowa sai k'unk'uni yakeyi."









  MG ne zaune agaban mai martaba da'alamu bakinsa akwai magana sosai amma haryanzu yak'i cewa komai. "
Ganin haka yasa mai martaba ya sallami duka 'yan palace d'in."
Juyawa yayi ya fuskanci MG, sannan yace "
Yareemana da' alamu bakinka akwai zance dayawa amma kayi shiru."
Maza fad'amun damuwarka kasan idanba niba bbu typing wanda yadace ka fayya cewa damuwarka. "
K'asa yayi da kansa yanad'an sosawa ganin haka yasa mai martaba murmusawq,"
Yanajin dad'i MG ya tambayeshi abu duk girman abun yana iya barmasa. "
Ehem go ahead my son tell me, yafad'a a lokacin dayake ta6a kafad'arsa,"
Cikin alamun Jin kunya yace "
Dama abba inaso aje nemamun auren *hanna* ne."
Mai martaba bayyi tsammanin zancenda zaifuto abakinsa bakenan, baisan lokacin da ya mike ya zauna daga ki shine giden dayake. "
Cikin zumudi yafara magana, son da gaske kake?"
Allah nagode maka daka nunamin wannan rana, "
Nayi farinciki wanda nikadai nasan irinsa."
Yareema akullum ganin nakeyi kawai kana fad'in kakusa aurene dan ka kwantar mana da hankali, dukda cewa hakan amma idan kafad'a hankalina yana kwanciya, amma yau Allah ne kad'ai yasan irin farinciki da nake ciki, Allah yamaka albarka kuma yasa Alabarka azamnatakewar auranku. "
Cikin ransa ya amsa da amin."
Fad'amun yar gidan waye, zuwa gobe nasa amin bincike, dukda nasan cewa bazaka ta6a za6ar macen da batada tarbiya ba amma hakiinane amatsayin mahaifinka nayi bincike akan ta da mahaifinta."
Cikin ladabi yace Abba ai 'yar gidan wan mahaifin matarda Abubakar zai aura ne. "
Ikon Allah kenan wato duk wannan tsawon shekarunda muka dauka, kasanda cewa tanada kanin mahaifi anan?"
Gyad'a kansa yayi eh abba. "
Rashin sanine aida lokacinda akaje tambayan na Abubakar da anhad'a duka."
Amma yanzu komai da zafi zafi akeyi barina kira modiibo."
MG ne yad'aga wayar yamasa dialing ring uku aka dauka. "
Cikin girmamawa ya gaida middibbo, ya amsa Cikin kulawa."




Moddibbo aminin mahaifin mai martaba ne tsoho mai farar aniya, kuma babban malami duk wata amanar da sarki abdallah yabar masa, sanda yatabbatar yacikasu. "
Bayani mai martaba ya koro masa,"
Sosai ransa yayi fari dan murna har sujjudur shukur sanda yayi. "
Cikin farin ciki yace"
Allah yacikaman burinmu dazafi zafi zamuyi komai,"
Ran auren Abubakar sai muyi magana. "
Kannan muci gaba da addu'a Allah yacika masa burinsa dan idannasa yacika namu yacika."
Ahaka sukayi sallama kowa ransa farii tass. "
Nan da nan mai martaba yafara kiran dangi abunnema yasamu," Cikin yan mintuna kowa sai kira yake dan gaskatawa. "
Ummii dabatasan labarin mayyake faruwaba, kira kawai take gani ta ko'ina."
Kashe wayar kawai tayi dan batasan surutu. "  ni saida abinma yabani mamaki sai kace wanda akace yau ne d'aurin auren."





Su *hanna*  ne tsaye a kofar shiga fadahh, rigima sukeyi dan sunce bbu wanda ya'isa yasa Su cire takalmi, sunkai kusan 30 minute a kofar wajen har takai ga yanzu wasu dogarawa sunzo da niyar korasu. "
Tana kallo captain bala dake biye dasu tundaga gida."
Wajen dogarawa taga yanufa, "
Magana yamusu sai gasu sun nufo wajanta,"
Suna zuwa aikuwa hakuri suka fara basu, kamar wanda zasu tsugunna. "
Sannan suka umurci d'aya daya musu iso."
Hakan kuwa akayi." Suna shiga nan kallo yakoma sama ai basu ta6a tunanin fadan babban gari bane acikinta. "  sanda sukayi tafiya mai nisan gaske kafinnan suka isa wani sashi mai d'an karan kyau."
Adai-dai lokacin MG yafito daga kofar mai martaba. "
Gabantane taji yayi wani mugun fad'uwa sakamakon had'a ido dasukayi."
Saurin komawa baya tayi tariqe hameeda gam. "
Shikuwa d'auke idonsa yayi kamar baita6a kallonta ba."
Gani tayi daga fitowarsa sojoji sun masa runfa, tunani dama wato agidan sarauta yake, yatsine fuska tayi Sannan tace shiyasa yafiya girman kai. "
Tsaki taja mtsww wanda har yafito fili Suka juya Suna kallonta."
Ganin ko'ajikinta batamasan tayiba yasasu juyawa sukaci gaba da tafiya. "
Shikuwa anasa 6angaren baiyi mamakin gainta anan ba dan yanada tabbacin aikota akayi."
Wani plat suka nufa mai shegen kyau, dan tsarin baiyi kama da tsarin gidan bahausheba. "
Sak yanda larabawa sukeyin gidansu duk glass."
Tsayawa yayi abakin k'ofar sannan yayiwa wata kuyanga magana akan tayi musu issoh. "
Wani falo tashigar dasu falon bbu tarkace dan mai shashin batacikason yawan kayaba,"
Sai dai komai na falon classical ne. "
Juyawa tayi zata wuce, Saurin tsayarda ita amira tayi sannan tace wurin labba mukazo."
Amsawa tayi da kayi sannan tashige wani sashi.
Kafin d'an wani lokaci anchika gabansu da kayan marmari dasu drinks,
Ko kallon wanda takawo basuyiba balle sannu ransu yakai kololuwa gun baci, dan rainin hankali tawani shanyasu. "



Aiko ba komai sai tazo takar6i aikanta dansu bazama sukazoyiba. "





Can kusan tak'ara ten minute akai sai gatanan tafito."
Dan lokacin har amira tamike da niyyar fita, " ganin bazatafi sa'arsuba yasa ransu k'ara baci,
Karasowa tayi Cikin sakin fuska, binsu d'aya bayan d'aya tayi tana hugging nasu Cikin murna, nan tafara magana, dan Allah ku gafarceni nashiga wankane, ita kuma tatsaya jirana batazo ta sanar da Ummii ba ku gafarceni. "
Duk cikinsu bbu wanda jikinta baiyi sanyi ba ganin yadda sukayi tsammani ba haka suka sameta ba."
Hanna ce tace wallhy bbu komai dama sak'one, anty samha ta bayar akawo miki,
Cikin fara'a tasa hannu takar6i aikan godiya take surfawa, duk da cewa wannan bawani abu bane, amma tayi appreciating sosai. "
 *_Hanna_* ce take satan kallonta ko tabbas kama sukeyi sosai da wannan mutumin,
Itama kyakkyawace ta ajin k'arshe ."
Saidai MG yafita kyau😜. " hameeda ce ta mintsini amira ta niyyar tatashi, amira tashi tayi,
Hava dan Allah badai tafiya ba?"
Eh wallhy muna sauri ne inji hameeda, to muje ku gaisa da Ummii, da kin gaisheta kawai daganan aika zamuje,
No aibazataji dad'i ba idanna fad'a mata, badan ransu yasoba suka nufi wani shashi, afalo suka sameta, wata kyakkyawar balarabiya suka gani mai kmada labba, tana kallonsu tasake fuska,
Sannan suka k'araso gaisheta sukayi, ta amsa Cikin sakin fuska,
Ummii kinga abinda suka kawomun, a'ah😃 to angode Allah yasaka, ta fad'a tana kallon *hanna* wanda tun shigowarsu yarinyar ta d'auki hankalinta, kuma tarasa dalili,
Tashi sukayi suka mata sallama,
Hava my doughters kujira zuwa jimawa mana, dan har Cikin ranta batasan tafiyar *Hanna*   jitakeyi kamarta dad'e da saninta, kud'i ta d'auko mai yawa tabasu amma bayadda batayiba sukak'i kar6a. "
Ganin hakanne yasa tayiwa labba magana, sai labba tajuya samun kanta tayi ta riqe hannun *hanna* dasuke niyyar fita, lallausan hanu mai taushi ne taji ya riqeta, saurin juyawa tayi sukayi idoh hud'u dana Ummii, saurin yin k'asa da kanta tayi dan haka kawai takejin nauyin matar, had'a idonda sukayi kuma yasa tajii wani iri kamar wanda tataba kallon kwayar idanun awani waje. "
K'ara damk'e hannun ta tayi my doughters, dagowa tayi tasake kallon ta sannan tak'ara sadda kanta k'asa,
Menene sunanki?"
Ita kanta batasan lokacin da tamabayar ta fito abakin taba,
 *Hanna* tfad'a Cikin girmamawa da jin nauyin wanda akeyiwa magana,
Alhmdllh tafad'a a zuciya a fili kuma tace, sunanki da dad'i, nagode tafada ahankali,
Juyawa tayi gunsu, amira nan ma ta tambaya kowa ya fad'a mata, albarka ta samusu, anahaka labba tafito, itada wasu kuyangi da ledoji a hannunsu, har lokacin hannunta na riqe dana *Hanna*  nan ma dakyar suka kar6a saida sukaga ranta ya6aci. "
Dakyar tasaki hannun ta hakan ba karamin mamaki yabawa Hanna ba,
Direba akasa yakaisu har gida, anan akayi tamusu fad'an kar6an kayan da sukayi."






Shirye shiryen fita event suka fara, mai kwalliya tazo Har ta fara shirya amarya sai a lokacin, su *hanna*   suka fara shiryawa suma. "



To be continued



Ur's
    ~Z33yyb3rw3r~
[12/2, 9:30 AM] Anty Jamila D Ili: *BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

My first novel


 _
_This Page is dedicated to Hon Bawa Alabura's family. "zaynab bawa loves u dearest, ina alfahari daku."_


Page 36



*
  K'arfe hud'u dai-dai sungama shiryawa, har amarya tagama."
Su *hanna* ne iyayen kad'ad'i haryanzu ana jiransu. "
Dayake bikin na mata ne yasa maza bazasu hallara ba ango ne kawai da abokansa akesaran zuwansu wajan."
Abokan ango sungama zuwa jira kawai sukeyi a futo musu da amarya. "
Duk wanda yakamata Su fito sun fitoh, ganin Su hanna basuda niyyar fitowa yasa kowa tafiya akabarsu sunanen sai wani kwalliya akeyi,"
Kwalliyarsu tayi matukar kyau sosai, dan gown ce daga waist tabud'e sama kuma k'irji takama sosai, long arm ce rigar,
Orange d'in material ne sannan sukayi head da bakin glass syton, sosai kayan ya musu kyau dan dama Su ba baya bane wajen d'auri, daura shi sukayi yayi kyau,
Bakin gyale akad'auko, aka d'aurashi a right shoulder, sannan kowacce ta kima prada a idonta, sai wani gamshi sukeyi barin *hanna*  datasha gyara, sai wani k'yalli takeyi, sosai suka fito yanda kasan 'yan uku saidai duk amira tafisu haske. "
Koda suka fita kowa yagama tafiya, tsayawa sukayi turuss, na mamakin ganin ko mota d'aya ba'abar musu ba,
Dan gaskiya bazasu hau taxi ba.'"
 *Hanna* ce taciro wayanta da niyyar kiran ya jalal, get d'in gidan mai gadi yabude,
Wata arniyar mota ce tafaso ciki,
Ash colour na 4matic ce. "
Sanda tazo dai-dai Su sannan ta tsaya,
Kollon motar suka tsayayi, dan black tinted ne aglass din motar,
Sliding down aka farayi labba ce aciki tayi kyau na fitar hankali, horn ta danna sannan tad'aga murya, beb we r already let lets go."
Back sit hameeda da amira suka shiga, sai *hanna* ta shiga front. "
Kan Su isah tad'i sukeyi kamar sun dad'e da sannin juna."
Suna isa hotel d'in suka nufi hall d'indq za'ayi diner, sosai hankali ya dawo kansu dan sun had'u ne bakarya. "
Kujerunsu Su hud'u suka zauna dan dama hud'u hud'u ne sit d'in."
Event yayi kyau sosai barinma daya samu hallarar manyan mata. "
Komai na decorating wajen da pich da fari akayi bakaramin kyau wajen yayi ba."










Ana fara lik'i sosai sukayi ruwan kud'i awajan, MG dama shikam baijeba, ba yadda Abubakar baiyiba amma saiyace d'aurin aure da diner kawai zai hallara. "
Su amira iyayen yawo aibasujira antashi ba suka, fice yawo."
Basu suka dawo gida ba saida akatashi awajen kowa ya watse. "
Ummii tayita zuba ido ko zataga *hanna* amma bata gantaba,
Su kuma abinda yasa basuyi wani rawar kai awajen Event d'inba, Event din manyan matane shi yasa suka ficewarsu kawai."
Suna shiga sallan magrib da isha sukayi,
Suna zaune ad'aki *hanna*  tajuya ta kalli Su sannan tace beb nifa gaskiya bazan kwana agidanna ba, gaskiya i can't, hayaniya yayi yawa."
Dan guntun tsaki hameeda tayi ni wallhy yunwa nakeji,"
Kuma gaskiya bazanci abincin gidan biki ba. "
Ke naji mama tanacewa Su hafast da rabi'ah Suna hanya kuma adakinnnan dasu zauna *hanna* tafad'a."
Amira najinsu ko k'ala batace musu ba. "
 *Hannace*  tajuya ta kalli wata katuwar hand back na amira Ke juye kayan nan kibani jakar nan."
Kollon tuhuma suka mata, " Ke da'allah bani kinji."
Juye kayan jakar tayi ta miqo mata, ta k'arba, ku tabbatar kun had'a mana kayan mu zuwa gidan adda hindu yau anan zamu kwana bbu musu hameeda tahau had'a musu ita kuma tasakai tafice."
Kaitsaye dakin umma tawuce, marai raice fuska tayi umma yunwa tafad'a kamar mai shirin yin kuka. "
Janta umma tayi ta kwanta ajikinta"
Srry mai dear mai zakici toh? "
Umma ko snacks ma, fulo ta d'aga tadauko door key's, gashi jeki dakin abbanku ki ebo miki, mama dake zaune sai lokacin tayi magana yanzu yaya abinda aka tanada dan bakin ne zataje da eba?"
Taci abincin gida mana. "
Tashi kitafi abinki kawai umma tace."
Fita tayi ta nufi sashin abba, sanda tagama eba musu snacks sannan da ebi drinks tafito. "
Ak'ofar dakin ta tsaya, beb kufito mutafi fitowa sukayi, sannan tak'ira yaya jalal, ba dad'ewa yqzo yakaisu, yana kaisu yasaukesu yajuya, shiga sukayi aranan anan suka kwana."






   Tunda gari yawaye najeeb yaketa farin ciki dan yau zai je kano gano masoyiyarsa,
Momy ce ta fahimci farin Cikin da yake ciki, son irin wannan farinciki haka sai kace wanda nayi suruka? "
Sosa kansa yayi ai Momy kamar kinsani yanzuma ganinta zanjeyi,"
Momy na dad'e bangantaba kitayani addu'a Allah ya mallakamin ita wallhy Momy insonta dayawa, "
Shafa kansu tayi cikin jin dad'i tace isha Allah takace my son, shiga daki tayi sannan tace barinazo, kid na makeup tafito dashi sabo fill, mika masa tayi gashi ka bata kai gaishemin da ita tashi katafi kar lokaci yak'ure kaga yanzu har 11:00."
Mikewa yayi yamata godiya sannan yamata sallama yakama hanya. " kusan k'arfe hud'u ya isa garin kano,
Gidan abokinsa yafara wucewa yayi gidan abokinsa, da sukayi karatu tare a US. "





Wajen k'arfe biyar basu gama shiri ba,
Abokan ango har sungaji da jira."
Sai Wajen 5:30 kafin suka fito aka nufi wajen kamu. "
Sosai amarya da angon suka had'e dan anty samha da Abubakar ba baya ba wajen kyau."
Su *hanna* ansha makeup da wani high hill ak'afanta, "
Anfara gudanar da event rawar kai awajen Su hud'unan ba'acewa komai, idan suna tafiya kuwa yanda kasan dasu b'alle dan rangwad'a,"
Kudi kam ba'a magana dan anzuba shi awajen. "
Sosai abin yak'ayatar da kowa, anfara kiran magrib, lokacin najeeb yatashi daga bacci, yana isa tsabar gajiya ya kwanta bacci yadaukeshi sai lokacin ya farka." agurguje yayi wanka sai wani zumudi yakeyi farin yadi yasa yayi kyau sosai,
Sai kamshi ne mai dad'i yake tashi. "
Shida abokinsa abba suka nufi gun event d'in,
Basu sha wahalan shigaba dan event d'in bamai tsauri bane, alokacin dayazo dai-dai kofar hall d'in alokacin gabansa yatsananta fad'uwa gawani irin farinciki dayake ciki, shiga yayi yafara rarraba ido wajen ganota,
A dai-dai lokacin da ya juya zuwa wani site alokacin ita kuma takalmin k'afanta yakusan yada ita, saurin riqota salman deke kusa da ita yayi,
Riqe k'uqunta yayi alokacin najeeb yakai dai-dai kallonsa wajen fad'uwar gabansa ne ya tsanan ta a yayinda wani irin bakin ciki ya maimaiye zuciyarsa jiyakeyi kamar ya had'iyi zuciya ya mutu dan bakin ciki, alokaci daya idanuwansa suka kad'a sukayi jaaa kamar gauta. "
Waigawa tayi bayan salman yasaketa aikuwa caraf idanuwanta suka sauka akan najeeb Cikin murna ta nufeshi, juyawa yayi ya fice daga wajan azuciye wata irin tsanarta ce ta mamaye zuciyarsa."
Binsa tayi abaya da d'an gudu-gudu, sauri-sauri, itama tafice, Can wajen da akayi parking car's taganshi yakife kansa ajikin wata mota, dasauri taqarasa wajen,
Tana isa ta tsaya cikin muryar shagwa6a tafara magana, yanzu myn shine baka sanardani zaka zo ba ko toh nayi fushi,  tafad'a had'eda juyar da kanta,
D'ago fskarsa yayi da mamakinta hawaye tagani wani yanabin wani, alokacin da suka had'a ido lokacin wata tsanarta ya k'ara mamaye shi, jiyakeyi kamar yashaketa ya kasheta. "
Cikin rud'ewa ta matso kusa dashi, myn mayya samek.. Bata k'arasa ba yakatsaeta idan kika kuskura kika matso kusa dani saina miki abinda bazaki tab'a zatoba, banza maciyiya amana, wanda tarbiya bai gama isarta ba kinyi asara aryuwarki ta duniya da lahira, dama ashe cutata kikaso yi bansaniba Allah ya nunaminke yau, Allah yafitar dani daga sharrinki, wallhy nayi dana sanin saninki. "
Wasu irin siraran hawaye ne suke bin fuskarta dan batasan mai tayiba yake mata irin wannan Cin mutumci hakan."
Ranta yayi mata zafi sosai amma tamatsa kusa dashi da niyyar bashi hakuri, "
Dan ko mai yamata batajin zata iya rabuwa dashi dan tana masa son da rabuwarsu zai iya hallaka ta."



   Fans kuyi hakuri da jina da kukayi shiru kwana 2, wasu uzuri ne suka tsareni. "
Luv u all my fans😍😘



To be continued


Ur's
     _Z33yyb3rw3r_
[12/2, 9:31 AM] Anty Jamila D Ili: *BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

My first novel



Page 37


 _ _Wannan shafin sadaukar Wane ga Duk wani masoyin BIBIYATA AKEYI,_
_Inasonku sosai,  muna mugun tare__ 😜 ."


**
    Matsowa kusa dashi tafarayi cikin zubar kwalla, dan ita bawai magan ganunsa bane suka d'aga mata hankali ba kamar yadda taga tashin hankali ak'wayar idanuwansa dan kokadan batasan tashin hankalinsa. "
Tazo daf dashi yace, karki kuskura ki zo kusa dani danna tsaneki."
Cikin tsiyayar hawaye tace myn wat terrible things have i done to deserve those horrible words? "
Kallan matsiyaciya ya bita dashi, Kallan raini da tsana."
Wato bakimasan mai kikayi b kenan? "
Cikin kuka tace,"
Dear am srry, despite not knowing wat really makes u dhat anger but am srr,,, katseta yayi no don't, "  don't srry me becouse i won't." stay out of mhay site na tsaneki yafad'a Cikin tsafi haded'a nunata."
Wuceta yayi ya shiga mata, yana jiran fitowar abba sutafi, "  shikuma abba yana ciki yana jiran sa yad'auka sunachan suna soyewa."
Dakyar da d'aga kafafuwanta da suka mata nauyi da niyyar komawa. "
Turus ta tsaya dalilin ganin mutum agabanta ya h'arde hannuwa, matsawa tayi ta d'ayan gefen zata wuce, saurin shan gabanta yayi,"
Cikin zafin zuciya yace hmm,  aini na d'auka mata marassa ajii sunk'are amma yau nagani da idanuwana dan banyi tunanin akwai macenda saurayi zaici mata mutumci haka ta zauna bashi hakuri ba. "
Ke kuwa wace irin macece?"
Numfasawa yayi sannan yace i wish am in ur shoes da saiyayi dana sanin, those f*cking words da ya ambata. "
Kallonsa ta tsayayi alamun magan ganunsa sunfara shiga jikin ta,"
D u knw wat bakuma dace dashiba, natabbata idan kika rabu dashi daki samu wanda yafishi. "
Naushi yakaiwa hannunsa sannan yace damn him."
Yana fad'in haka yajuya yashige ciki kallo tabishi dashi dan batasan wayeba. "
Amma ku masu karatu yakamata kusan waye bakowa bane captain Ahmad ne."
Amma magan ganunsa Duk sunshiga jikinta. "








Juyawa tayi tanufi wajensa,"
Kwankwasa glass d'in car d'insa tayi, "
Yakifa kansa ajikin sityerin motan kaman mai yin kuka."
Jin knocking yasa shi d'agowa, ganin itane Cikin tsafi ya bud'e motar ya fito, Cikin hasala yafara magana,
Ke wacce irin jarabbiya ce?"  hah banace kirabu dani b,,,,,,    bai rufe baki ta tasauke masa wasu tagwayen mari guda biyu. "
Cikin d'auriya tace, kaine autan maza?"
Shiru yayi dan bazai iya kallon idonta ba
Tsareshi tayi da ido Cikin tsafi tace tambayarka nakeyi kaine autan maza? "
To koyau aka haifeka narabu dakai har abada."
D'ago idanunwansa yayi dasauri ya kalleta, "
Eh ka kalleni dakyau, nayi danasanin had'uwata dakai, nayi dan danasanin soyayyarka,"
I regret every bit of our relatolionship,
Sake d'agowa yayi ya kalleta da idanuwana dasuka rine, "
Kana mamaki ne?"
I mean it, i regret every single bit of it."
Dakayi danasani kuma na tabbata lokacin zaizo maka a kurerren lokaci. "
Yhou knw wat?"
I hate yhou either. "  is over" between us."
Tana fad'in haka ta juya zuwa ciki."







Mamaki ne fall aran captain Ahmad akan tayaya hakan ta kasance, tabbas yasan su captain bala suna iya kokarinsu, Amma kuma faruwar hakan ya bashi mamaki. "
Dole yab'oye Wannan maganar karyakai kunnen MG dan Ahmad kamar yasan mai zai faru."
Nisawa yayi sannan afili ya furta yanzukam ai komai yazo karshe. "
Juyawa yayi ganin itama tajuyo da niyyar shigowa."
Can wani waje tanema ta zauna, yanda bbu wanda zai ganta."
Gabaki d'aya hawayen idauwanta ya d'auke. "
Zuciyarta sai wani irin zafi take mata, so takeyi ko sau d'aya tayi kuka har inde zafin zuciyarta zai ragu."
Ba irinneman da su hameeda da labba basu mata ba amma basu ganta ba, "
Hankalinsu yatshi sosai,
Can da taga zaman bayi mata dad'i takira salman awaya akan yazo ya kaita gida, fita tayi ta tsaya ajikin motarsa baifi 15 minute ba yakaraso, shiga tayi yaja suka tafii."
Suna tafiya ba irin tambayar da bai mataba amma ko kallo bai isheta ba, suna isa tabud'de mota tashige gida ko rufewa bata tsaya yiba. "
Afalo ta samu anty hajja da anty maman amal sunzo."
Dakyar ta iyace musu sannu tawuce, dan wani irin haushin maman amal ne yakamata ganin cewa aik'anin mijinta ne. "
Kallon Mamaki suka bita dashi kawai bbu wanda ya iya cewa komai,"
Tana shiga daki tasamasa key, ta kwanta zuciyarta namata zogii. "
Shikuwa najeeb na komawa gida yarasa maiyake masa dad'i, shi kwata-kwata baisan mai tayi Dayayi mata irinn Wannan Cin mutuncinba." Kokad'an Wannan kalaman daya futo abakinsa badaga zuciyarsa takeba, Cikin zuciyarsa soyyarta ne a cike, magan ganun kamar wanda aka matse bakinsa, yarasa dalilin dayasa ya furtasu amma kuma bayajin zai iya bata hak'uri, shiga dakin abba yayi ya kulle kansa kuka yakeyi kamar karamin yaro,
Tashi d'aya wani irin zazzab'i ya rufe shi karkarwa yafara yi, nan take yafara fita hayyacunsa. "
Ganin Shiru yasa abba yabuyoshi, ganin halinda yake ciki yasashi kiran doctor bbu shiri."
Su amira bbu irin neman da basuyiwa *hanna*ba amma Shiru bbu ita bbu alamunta, dan har hameeda tafara kuka, labba da amira  kuwa ba'acewa komai,  itakam labba shiga cikinsu da takeyi ma dama dan *hanna* ne haka kawai Allah yahad'a jininsu. "
Har kowa ya watse awajen amma sukam sunk'i amrya ma da taji meke faruwa kawai sai tak'i tafiya, idanuwanta sukayi jaaa sosai kana kallon kasan tayi kuka ko tanaahirin yiii."
Ganin mutane sun dawo ne su basu dawo ba harkusan isha yasa umma kiransu, dakamar bazasu fad'a mataba daga baya suke fad'a mata mai yake faruwa. "
Rike baki tayi tayi salati sannan tace musu ai *hanna* tafi 3 hour's agida."
Cikin alajabi suka dawo, dan ko bata da lafiya ne, Dakyar suka lallashi labba ta koma gida datace" saita bisu ga dare yayi. "







Suna shiga gida dakin suka nufa, tun suna bugawa hankali kwance abu kamar wasa har hankali yatashi bbu irin bugun da basuyi ba amma taki bud'ewa, tsabar rikicewa Dakyar umma tagano extra key's na d'akin tazo ta bude."
Lokacin su amira ansha kuka kamar ransu zai fita. "
Ganinta azaune akan sallaya yasasu sauke ajiyar zuciya."
Cikin kuka amira da hameeda suka nufeta rungumeta sukayi sannan sukaci gaba da kuka. "
Kallonsu d'aya bayan d'aya tayi sannan aranta tace ku dad'i ma kukeji tunda harkunsamu damar kuka."
Shigowa sauran sukayi tambayar duniya bbu wanda basu mata ba amma taki tankawa."
Tsaki mama taja tafice abinta, haknne yasa umma matsowa ta rungumeta, tafara lallashinta sai alokacin tasamu bakin kuka, kuka kawai takeyi bbu wanda yatsareta, ganin haka yasa hafsat da rabi'a suma Jan tsaki suka fice adakin ".
Sanda tayi mai isarta umma sai shafa mata baya takeyi sai Can ta kalli umma tace"
Umma mai na tsare musu? "
Umma wallhy insonsa amma sun rabamu, Cikin rikicewa umma tace suwaye?" idanfa bakin tsaya kinyi min bayani ba bazan gane ba. "
Nan takoro musu duk abinda yafaru yau da irin zaginda yamata."
Bawanda ransa bai baci ba ad'akin, barin anty maman amal datasan cewa k'anin mijinta ne jitayi dagashi har yayansa haushi suke bata. "
Matsowa samha tayi ta riqe hannuwanta sannan tace asiff habibty, ai nafad'a miki kika k'i yarda dani alokacin gani kikeyi kamar wanda son rabaki nakeyi dashi."
Kayya anty samha dama tafad'a tace in tana raye bazanyi aureba, Cikin kid'imewa umma tace wacece Shiru tayi, ta sunkuyar da kayi, hameeda ce tabata labarin komai, Cikin matsanan Cin bacin rai tafara masifa, lallai tabbas halima ta isa,
In sha Allahu sai Allah yamana sakayya. "
Tana fad'in haka tace 'yata share hawayenki in sh Allahu sai kin auri mijin nunawa duniya."
Tana fad'in haka tafice Cikin k'unar rai. " haka suka zauna sukayita rarrashinta har tayi bacci."








   Washe gari ma Dakyar taje walima."
Shikuwa najeeb ya d'an samu sauki aikuwa yace shi gida zaikoma, bayadda basuyi ba ganin haka yasa abba yi musu driving komawa garin bauchi, "
Itakuwa labba tana komawa duk aburkice yasa ummii tamabayarta mai yafaru tana fad'a mata taga ummii tafita birkicewa, tsayawa kallonta tayi, ummii ya haka menene ya faru,
Ai batad'au lokaci ba ta shaida mata tanaga kamar itace yarinyar da yayanta yakeso dukda bata da tabbaci amma tanada yak'inin hakanne, ai labba najin haka tafashe da kuka dakyar ummii ta rarrasheta, kiran wayar amira tayi tana d'auka tafara tambayarta *hanna*  shaida mata tayi batajin dad'i ne yasa ta koma gida da wuri amma yanzu tayi bacci. "
Aikuwa sassafe labba tashirya zuwa gaida ita, sallama tayiwa ummii tafita jitayi kamar ta bita taga jikin amma dai haka sukayi sallama tabata aika takai mata."
Haka aranar tare suka inii da *hanna* ko awajen walima ma hannunta yana jikin na *hanna* . "
Yau takashance Saturday ranar d'aurin aure sai shirye shiryen d'aurin aure akeyi inda k'arfe 11:30 za'a d'aura."





To be continued




Ur's
 _z33yyb3rw3r_
[12/2, 9:32 AM] Anty Jamila D Ili: *BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

My first novel

  _Fans ga garon sallan ku, gaskiya yau bansoyin typing ba amma naga yakamata abaku garon sallah eid mubruq dearest_

Page 38


*

   Yau takasance ranar asabar, ranar d'aurin auren samha da Abubakar. "
   Wanda za'a daurashi k'arfe 11:30."
  Tun safe hankalin *hanna* yake tashe sakamakon kiran da abba abokin najeeb ya mata, " yashaida mata cewa najeeb nakwance a asibiti bbu yanda yake dan ko mutane baya iya ganewa."
 Bata k'arasa jin mai zai fad'a mata ba takashe wayan kuka tayi sosai wanda har fuskanta da idanuwanta sun kumbura, sunyi jazir fuskan ta yayi luhu luhu. "
   Tun safe ko abinci bata iya cii ba ko ruwa batasa abakinta ba."
  Muryarta gabaki d'aya ya dashe dan kuka gabaki d'aya tausayin Najeeb ne yacikata tasan ko meye yasameshi itace sanadi. "
   Kuka takeyi ad'aki kamar ranta zai fita, tana kuka tana cewa kayafemin dear wallhy nayi danasanin saninka har nasaka acikin wannan halin, kayafemin."
  Har kusan k'arfe goma 10 umma tashigo tasameta Ahaka, dkayr ta rarrasheta,
Umma najeeb ba lpy   umma natsani kaina najeeb yashiga wani halin ta dalili na. "
Shhhh my doughter bakene sanadii ba Allah yarubuta hakan sayya faru."
Maza tashi kije ki k'ara yin wanka maza kinji 'yata Ahaka tayi ta rarrshinta hartayi wanka tafito, kaya ta za6o mata tabata ta sanya amma ko powder batasa afuskanta ba. "








  K'arfe sha daya da rabii 11 :30 aka d' aura auren samha yusuf dambam da Abubakar umar waziri akan sadaki duba dari lakadan ba ajalan ba."
    Bayan and'aura can na hango MG kusada ango kaikace shine wannan ango a irin kyau da yayi, fararen kayane k'all ajikin sa, sai fara'a yakeyi yasan yau tabbas mai martaba da moddibbo zasu nema masa auren *hanna* abinda ya dad'e yanajira shekara kusan goma. "







Bayan angama d'aurin auren, mutane sun watse  sosai saura d'ai-d'ai ku,
Moddibbo ne ya kalli baban *hanna*  wanda ko ba'afad'abaa sunsan shine mahaifinta danshi yakar6i auren samha ma."
 Cikin mutumtawa suka k'ara gaisawa, sannan ya d'aura da cewa, in sha Allah hu akwai maganar da nakeso muyi amma kuma tun da mune masu nema nafiso mubika zuwa chan Bayan kakoma. "
Dan murmusawa baba yayi sannan yace ai tunda Allah yahad'amu anan sai muyi kawai basai kunje ba aikomai sauki ake nema,
Da mamakin su mai martaba ne ya amshe maganar wanda a iya saninsu saidai dogarawa suyi magana amma shi baicikayi ba."
A'a dakun bari dai mubiku tunda mumuke neman arziki sai mubika har mazuninku mu nema yafad'a had'eda fad'ad'a fara'ar fuskarsa. "
 Jin haka yasa sukasan maganar mai matukar mahaimmacii ne."
  Abba ne yad'an gyara zamansa akasan dayake sannan yace, Allah ya huci zuciyar ranka shi dad'e bawai naja da maganrkaba ba amma ai anan d'in zqifi sauki, Allah yahuci zuciyar ka,
Shiru mai martaba da moddibbo sukayi wanda sukansu sunfi san hakan amma hakan dasukayi shizai nuna damuwarsu da abun. "
 Moddibbo ne yayi gyaran murya sannan yace to hakan ma yayi,  amma sai mud'an sami wajenda bbu matane."
Tashi sukayi dukansu da waziri da mai martaba da moddibbo suka wuce gidan Abba, kai tsaye falon Abba suka wuce. "
Zama mai martaba yayi shida moddibbo akan kujera yayinda Abba da baba suke kokarin zama ak'asa."
  Saurin tsaresu mai martaba yayi A'a katashi kuzauna a kujera kada kud'aukeni a matsayin shugaba ko wani mai mulki ku d'aukeni qmatsayin ubanda yazo nemawa d'ansa aure. "
Had'a baki Abba da baba sukayi suna tambayar aure?"
  Moddibbo ne yace kwarai kuma a yarima mukazo nemawa auren d'iyarku, gaba ki d'aya tunani nasu ne yatsaya a iya tunaninsu sunsan d'ansa yarima shine sojan da duk kasar guda d'aya akedashi, kuma kakansa ne mai shagon gwala gwalan dasukafi kowanne ak'asar dubai (abu-dhabi). "
To kuma me zayyi da d'iyarsu??  Mutuminda saninsu ko'yar sarkin saudi yanema zai samu."
Kansa ne ya d'aure, shirunda sukayine yasa moddibbo tamabayar ko kunyi mata miji ne??"
   Girgiza kai Abba yayi gumina tsattsafo masa, dan yanzu baba yafara tunanin hameeda akazo neman aure. "
 Bayaninda da moddibbo yafara ne yak'ara hargitsa musu tunanin,"
 Idan kun amince muna nema masa auren yarku *hannatu*  wanda yad'au tsawon shekaru yana dakon sonta, adalilin tana yasa har yanzu baiyi aureba. "
Koda anahaka maganar aure yakan shaida mana yanada wacce yakeso tun muna d'aukan abin awasa harmuka dawo tunanin ko aljance ta aure shi Iya addu'a da rokon Allah munyi amma ko sau d'aya baita6a budan baki yace mana ga garinda yarinyar takeba. "
Koda sunanta bai ta6a ambata ma wani ba."
  A'ina gayanta shikadai yabarwa kansa sanii dan baima zauna da wani yayi labari ba balle ya fad'a masa, abinda muka sani shine kawai yana matuk'ar sonta, ak'alla shekarunsa 35 aduniya amma har yau baiyi aureba da'an masa magana zaice lokaci yake jira."
Kuma bana tunanin yarinyar tasani. "
  Abba da baba sunrasa awani yanayi suka tsinci kansu farinciki ne kokuma akasin haka."
  Shiru Abba sukayi sai can yace hakika wannan lamarii akwai rud'ani aciki, baznce kunyi batar kaiba amma fa yarima kukace da d'iyarmu. "
Allah yaja ran mai martaba, kunsan cewa dai yafi k'arfinta kokadan shiba sa'an auranta bane ina yariima ina *hanna*."
Mai martaba akan yaji zafin maganarsu sai ma sanyi dayaji aransa, dan ba kowa bane za'a ce sunje neman aure yafad'ii wannan maganar ba, "  Sai marassa son abun duniya,"
  Gyara zama mai martaba yayi sannan yace, har inde kun amince ku kira yarinyar mujita bakinta. "
  Shiru sukayi dan tunda dakansu sukazo bbu dad'ii ace basu amince musu ba."
  Abba ne afili yace Allah ya za6a mana mafi alkhairi, hakan kuwa yafaranta musu rai alamun sun amince. "
d'aga waya yayi yakira umma cemata yayi kuturomin *hannatu* ina falo  na yanzu,  sannan yakashe."
  Umma dake gefen hannatu ne tajuya ta kalleta,tashi kije abbanku nakiranki yana falo. "
Ba gardama ta tashi ta zura k'atoton hijabinta har k'asa sannan tafice."












 A k'ofar shiga falon ta tsaya tayi sallama ciki ciki, amsa mata akayi sannan tasa kai tashiga kanta akasa hango Abba da tayi agefe yasa tanufeshi dan batayi tsammani akwai wasu afalon ba ko kadan bata lura ba. "
  Gaban Abba tanufa taje ta zauna sannan tace abbana gani,"
  Tunda ta shigo falon mai martaba waziri da moddibbo suke kallonta hak'ik'a yarinyar nada hankali kodaga tafiyarta ya nuna hakan mai martaba ne yaji yarinyar ta kwanta masa arayi sosai, "   kqllon fuskanta akumbure yasa ya riqo hannunta 'yata mai yasameki?"
 Jin haka ne yasa baba kallonta tabbas fuskanta akumbure yake alamun tayi kuka, "
Sunkuyar da kai tayi Abba kai nane kemin ciwo, kinsha magani ya tambaya gyada masa tayii,"
Ga baba fa yazo nan baki gaidashi ba, "
Azatonsu murna dasu kallo tayi amma saitaki d'agowa ta kalleshi, dan tasan tabbas idanta tad'ago zai fahimcii tana Cikin damuwa,"  *hanna*  bakiji mai nace bane ahankali tace ina wuni baba sannu da hanya, "   bai amsaba yaci gaba da kallonta, moddibbo yak'ura mata ido akwai abinda yake tunani akwai abunda yakeso ya tabbatar agame da ita."
  *Hanna*  babanta yakira sunanta d'agowa tayi ta kllashi, kinga wayannan mutanen sai a lokacin ta d'aga ido ta kallesu, gaishesu tayi suka amsa da fara'a, "
Neman aurenki sukazo, ai a lokacin kukan da take maqalewa ya kufce mata, Cikin kuka ta rarrafa gaban babanta, tariqo hannunsa, tana kuka tafara cewa baba kayi hakuri karkasa wasu acikin damuwa kawai kabarni nazauna Ahaka kamar yadda takeson ganina baba kacikaa mata burinta kawai, kar wani yak'ara cutuwa ta dalilina,  tunda ta fad'a baba kabarta ta aikata kawai tana fad'in haka kuka tacii k'arfinta aguje ta tashi tafice moddibbo ne yatashi yabi bayanta aka bar su baba da tarin tambayoyi aransu. "





To be continued



Ur's
     Z33yyb3rw3r

[12/2, 9:31 AM] Anty Jamila D Ili: *BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

My first novel



Page 39



*
    Bata nufi ko ina ba sai garden tazauna akan resting chairs, sai kuka takeyi, kamar wanda danshi aka aikota duniya. "


    Ganin yanda take yasa moddibbo nufan wajen, tsayawa yayi ya gama nazari akanta, dafa kanta yayi, daogowa tayi takalleshi farine soll tsoho mai farin gemu yanada tsayi madaidaicii,"
Sunkuyarda kanta tayi dan wani irin kwarjini yamata, "sunkuyawa yayi ya zauna da nishi alamun tsufa ta kamashi,"
   Cikin sigar kwantarda hankali yafara magana irinnasu na dattawa,"
Jikata nasan kina Cikin damuwa amma kisani kuka ba shine mafita ba. "
Akullum ki yawaita addu'a shine maslahar damuwarki, sunkuyarda kai tayi ta cigaba da wasa da yatsunta,"
Murmushi irinnasu na manya yayi sannan ya cigaba da cewa, mai nene dalilin da zaisa iyayenki su za6a miki miji amma ki bijre musu? "
Sunkuyarda kai tayi hawaye d'aya nabin d'aya sai yanzu take danasanin maganganun data fad'a musu kuma agaban wa'yanda sukazo neman auranta."
Baijira amsarta ba yaci gaba da cewa, "
Kinsan cewa bbu wanda yake da mahimmanci a rayuwa irin mahaifa, kikasance Akullum mai san faranta musu,"    girgiza kanta tafarayi hawaye d'aya nabin d'aya, "    ahankali ta furta ba haka bane,"
Toh menene Jikata?"
Yatambaya Cikin sigar lallashi, "
Girgiza masa kai tayi, Murmushi yayi dan tabbas yasan akwai abunda take boyewa."










To kifad'amun dalili har inde bakyaso nazargeki akan kin yiwa mahaifanki biyayya, "   bansan cutarda wanda yake tareda nine ko kadan banso wani yasake cutuwa kamar yadda najeeb yacutu,"
K'ura mata ido yayi nasan gaskanta abinda yake tinani,"
Cikin hikqma yace kidaukeni matsayin kakanki, danni nadaukeki ajikata kifada mun duk wani abinda yake faruwa da rayuwar ki karki boyemun komai, in sha Allah tare zamu nemo mafita, "
Cikin yarda da tsohon tafara bashi labarin duk wani abinda yafaru har izuwa kwanciyar najeeb a asibiti, dogon numfashi yaja sannan yace mata, jikita tunda naganki nasan kina tareda sihiri ajkin ki saidai baida k'arfii dan atunanina yawan addu'a da kike ya ne yasa abin baiyi karfii ba amma in sha Allahu da addu'a zamu yakesu bbu wani abinda yafi karfin addu'a, " _mutane musani bawai dan kinada damuwa sai jitafi wajen wani yace zai miki aiki awarware sihiri shine masalaha ba A'a akwai addu'oii dayawa acikin qur'anii mai girma wanda su kadai sukan iya samawa dan adam waraka dan Allah mukiyaye zuwa gun wasu malaman yawancinsu bokayene suke k'arya dasunan malamai Allah yakare_





Nasiha yamata sosai sannan yace ga addu'a kiringa karanta ta kartabace abakinki da yardar Allah duk wani mai nufan ki da sharri zai koma kamsa ```waraddal lahul lazina kafaruh bigaizihim lam yanalu khaira wakafal lahul mu'umininal qital wakanal laahu qawuyan azizan hakima```
Wannan addu'a hakika tana maganin sharri dakuma mai nufinka da sharri ahaka yayita mata nasiha sannan yace taje tasamu mahaifanta tabasu hakuri, "
Jikata d'agowa tayi tayi kalleshi, gobe kizo gidana ki kar6i sauran addu'oiin, sannan zansa ayita saukan alqur'anii,"
Sannan abu na karshe bawai danna fito a dangin abadallah ba yakasance yaro mai hankali, duk duniya banda mahaifanki banga wanda zaisoki sama dashi ba, "
Yasoki tun baki mallaki hankalin kankii ba, yasokii tun bakisan kankii ba inatunanin duk wanda zaki aura abayansa yake amma inaso kiyita addu'an zabin alkhairii,"
Allah ya miki albarka amin ta amsa d'an hira suka ta6a sannan yatshi har bakin kofan tarakashi dake yatsufa ahankali yake tafiya sanda suka isah bakin falon taja tatsaya alamu yamata akan tashiga bbu musu tashigo shima yabi bayanta abakin kofa tatsaya ta durqusa guiwaowainta duka biyu sannan ta sunkuyarda kanta, "
Cikin rawar murya ta ce abba dan Allah kuyafemun nayi kuskure amma in sha Allah bazankara maimaita kamarsaba."
Mai martaba ne yayi magana wanda dama tun maganarta tafarko Bata 6ata masa raiba yasan dole da dalili, gashi yanzu yanda tatsuguna tana neman afuwarsu yasa yarinyar k'ara shiga aransa, Cikin sigar gamsuwa yace tashi kice d'iyata baki mana laipyn komai ba Allah yamiki albarka ahankali ta amsa sannan tatshi sum sum tafice, "  mai martaba suka fito sun tsaida zancen su na iyaye kowa ya amince amma sunaso yaran su dai-dai ta kansu, godiya mai martaba yayita musu Ganin haka yakarasa suka tabbatar lallai wannan al'amari nada mahimmancii."





   Karfe hud'u aka fara shirye shiryen d'aukan amarya Motoci ne nagani na fad'a akalla sun kai motoci ashirin kowacce baka ne wulik sunyi parking suna jiran fitowar amaryarsu,"
Itakuwa tana ciki ana mata nasiha sai kuka takeyi, kamar wanda akayiwa mutuwa dakyar aka fita da ita da matanda sukazo daukan amarya mamane riqeda ita suka shiga, "
Fada suka wuce dan anan zata zauna zuwa gobe akaita gidanata,"
 *Hanna* kuwa nad'aki iyakacin hameeda ne tabisu, iya karrama an karramasu, a shashin waziri umar iyayen abubakar aka ajijeta kafin agama biki, shashin yahad'u sosai, site d'in abubakar aka ajiye amare. "
  Sannan wa'yanda suka kawota suka koma gida."






   Karfe kusan 6 labba taga bbu *hanna* bbu dalilin zatajo gashi, bayan magrib za'a fara shirin dinner, "
  D'aukan motanta tayi ta nufi gidan dakyar ta lallashi *hanna* tabiyota dan itada tace bazata ba."
Da'akazo wajen shiryawa ma sanda akayi rikici ce  tace bazatayi kwalliya ba kuma su hud'unsu sanda ummii ta d'auko musu makeup artist,
Sanda suka addabeta ne yasa tayarda aka mata light makeup amma bakaramin kyau tayiba."
  9 aka fara tafiya wajen dinner, su *_hanna_*  sune k'arshen tafiya alokacinda motarsu tatsaya a katafaren hotel d'in alokacin motocin MG suka danno hancinansu Cikin hotel d'in. "








Fitowa sukayi amotan


_ Suka nufi ciki shima MG Fararen kaya yasa manya bakaramin amsarsa su kayi ba gabaki d'aya sai daukan idanuwa yakeyi, "
Amfara gudanar da event kowa yana sha'aninsa banda hanna data takure agefe bayanda ba suya tafita ba amma tak'i."
Shikuwa MG gabaki d'aya ya gundura da zaman wajen gashi ba kalli *hanna* ba kuma andameshi da kallo barin 'yan matan dake wajen, " duk da akayi akwai wasu daga Cikin sojojinsa a wajen amma hakan bai hanashi takura ba,"
Sanda event yakai tsakaiya aka kira k'annen amarya kowa yaje amma banda ita ganin yanda amaryar ta 6ata rai take kollonta yasa ta d'anji bbu dad'ii jakar kud'in tadauko ta nufi gun amaryar liki tafara mata sai alokacin MG yaganta yashagala da kallonta ga wanikyau da tayi sai dai fuskarta akwai alamun damuwa duk sai yaji bbu dad'ii ganin ta Cikin damuwa atunaninsa ko zancen auransa da aka mata ne yassata Cikin wannan damuwar. "






Bata ankaraba sai ji tayi kawai anfara mata ruwan kud'ii na liki kamar itace amaryar."






To be continued


Ur's
   *Z33yb3rw3r*
[12/2, 9:32 AM] Anty Jamila D Ili: *BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

My first novel

 

Page 40


*
   Juyawa tayi dan ganin wayake yimata manni ganin ya jalal yasata sakin murmushimurmushi ahankali tace,"   yaya ina kashiga?"
Bana ganinka, dan ta6e baki yayi, "
Banason hayaniyane yasani barin gidan,"
Sai kun gama bikinku zandawo, "
Harda saleem ko?"
 *Hanna*  tace eh yace mata atakaice,
Sanda yazo dai-dai kunnenta ya rad'a mata kinyi kyau d'an murmushi takarayi, yad'an kama ha6ansa🤔 ya kalleta kamar maisan gano wani abu a tattare da ita amma kinrame kad'an, mai yake damunki? "
Narai narai tayi da fuska alamun batasan tambayan,"
Ganin haka yasashi jan gyalenta ya nufii wata kujera da ita."
Alokacin ran MG inyayi dubu ya6acii har wani hucii yakeyi gashi idanuwansa sunyi jazirr. "
Jiyake kamar yaje ya shaqe jalal,"
Murmushin data masa yatsaya masa arayi gashi yawani ja mata gyalenta ita kuma tabishi. "
Runtse idanuwansa yayi kawai yana fitarda hucii mai tsafii."
Dakyar ya iya fita ya yiwa ango da amaryarsa liki, "
Yana tashi kallo yadawo kansa."
Daga nesa mutane keta d'aukansad'aukansa a photo dan wanda basubasu ta6a kallonsa bama yau sun kalleshi ba'a TV ba, balle masu pics wanda sunsan dasu samu kud'ii kowane mai photographer, burinsa ya d'aukeshi."
Dakyar yatsaya suka d'auki pics da couples d'in amma yahad'e girar sama data k'asa. "
Kusan 12 akagama diner, hanna tace ita dole gidan su zata wuce dakyar labba ta rarrasheta tayarda ta bisu shshin ummii suka nufa lokacin dare yayi sosai yasasu wucewa d'akin labba,"
Wanka suka fara yi sannan suka kwanta. "😴







    Najeeb an sallameshi a asibiti jikinsa yad'anyi sauki saidai damuwace fall arayinsa danko abinci baya iyacii balle magana,"
Iya tambayoyin duniyarnan ammasa amma bbu amsa duk 'yan uwansa hankalinsu yatashi ganin halinda d'an uwansu yake. "
Koda yayansa yakira anty maman amal Bata fad'a masa tasan komai ba saidai tad'an canja muryarta bakaman yadda yasaba jiba sai yabar hakan a hidimar biki."




   Washe gari da safe ko karyawa basuyiba *hanna*  tasa labba dole sanda takaita gida. "
Ahaka tatashi takaita,"
Ummii na falo taga shigowar labba, "
Cikin gajiya tazube akan kujera," 
Ummii ne tace habibty daga ina haka da sassafennan? "
Wallhy ummii *hanna* ce tace saina kaita gida wai zataje tasha magani batajin dad'ii,"
Cikin nuna kulawa da damuwa ummii tace Allah yasauwake, "
Ameen ta amsa atakaice."





K'arfe uku suka fara shirin yin bud'ar kai wanda za'ayishi acikin fada. "
Saikusan 4pm kafin akagama shiryawa,"
Alokacin hanna tadade da isowa Bata wani dad'e awajenba da damu labba tatashi tarakata wajan moddibbo, "
Ba su d'auko lokaciba suka dawo dayake addu'oii kawai suka kar6o,"
Sannan suka juyo. "
Sunsamu angama kawai suka wuce gida hardasu amira," wanda gobe zasu koma, "
Labba ne tasamu ummii adaki akan sallaya ta idarda sallah."
Sannu ummii, "
Yawwa Sannu inakika shiga?"
Naraka *hanna* kun moddibbo ne, "
Murmushin tayi danko sunan *hanna* aka ambata takanji son yarinyar aranta."
Yanzu wajen mai martaba zanje naji zancen yanda suka tsaya akan zancen jiya sunje tambaya, toh tunjiya bamu samu dama munyi zancen canba shiysa yanzu zanje, "
Murmushin fuskar labba ne yafad'ad'a, Allah yasa andace amin tace."
Sannan tamike tayi shashin mai martaba afalo tasamu mai martaba. "
Cikin fara'a da girmamawa tagaidashi,"
Cikin tsolaya tace nabiyo sawu ne, dariya mai martaba yayi sannan yace ohh uwar yaro ba hakuri anaso aji yanda zance yakaya."Murmushin tayi sannan tace  bakasan yanda yaronnan yake zuwa yazaunamin ba Koda bai furta ba amma nagane nufin shi. "
  To ai muntsaida zance da iyayen yarinyar amma munaso yaran su dai-daita kansu yanda abun zaizo Cikin sauki."
To Allah yasanya alkairi aciki da amin ya amsa Suna Cikin zancen saiga MG yashigo da sallama amsawa sukayi sanna yasamu wajen yazauna gaidasu yayi suka amsa masa. "
Zama yayi nan mai martaba ya labarta masa yanda sukayi da mahaifan yarinyar."
Wani irin fad'uwa gabansa yayi danshi yana shakkar tunkararta baisan mai zaifaru ba. "
Murmushin ya kakalo sannan yamusu sallama da godiya yafita."
ya yanke shawarar jibi ya tunkareta dan yasan rana mai mahimmamci ne arayuwarta. "
Da safe su amira da mama suka fara shiri jitaayi duk garin bbu dad'ii daga ita har hameedan, dan da tafiyar da *hanna* za'ayi amma tafasa batason abinda zai had'ata da Najeeb kokadan kuma tasan har inde tatafi zasu iya had'uwa."
Babe yanzu jibi nefa birthday d'ina wednesday amma bazaki zauna ba? "
Srry Beb wallhy mom ce tatakura Nima banso komawaba,"
Badan ransu yasoba su kayi sallama su amira suka tafi, kuma duka bakin sun watse sai d'ai-d'aiku. "
Haka sukaji wani irii bbu amira arannan sunyi bacci sosai, wanda tunda akafara bikin basu sameshiba,"
Washegari sukaje sukayi odering duk wani abunda zasu buk'atq gobe. "





To be continued




Ur's
     _Z33yb3rw3r_
[12/2, 9:31 AM] Anty Jamila D Ili: *BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

My first novel



Page 39



*
    Bata nufi ko ina ba sai garden tazauna akan resting chairs, sai kuka takeyi, kamar wanda danshi aka aikota duniya. "


    Ganin yanda take yasa moddibbo nufan wajen, tsayawa yayi ya gama nazari akanta, dafa kanta yayi, daogowa tayi takalleshi farine soll tsoho mai farin gemu yanada tsayi madaidaicii,"
Sunkuyarda kanta tayi dan wani irin kwarjini yamata, "sunkuyawa yayi ya zauna da nishi alamun tsufa ta kamashi,"
   Cikin sigar kwantarda hankali yafara magana irinnasu na dattawa,"
Jikata nasan kina Cikin damuwa amma kisani kuka ba shine mafita ba. "
Akullum ki yawaita addu'a shine maslahar damuwarki, sunkuyarda kai tayi ta cigaba da wasa da yatsunta,"
Murmushi irinnasu na manya yayi sannan ya cigaba da cewa, mai nene dalilin da zaisa iyayenki su za6a miki miji amma ki bijre musu? "
Sunkuyarda kai tayi hawaye d'aya nabin d'aya sai yanzu take danasanin maganganun data fad'a musu kuma agaban wa'yanda sukazo neman auranta."
Baijira amsarta ba yaci gaba da cewa, "
Kinsan cewa bbu wanda yake da mahimmanci a rayuwa irin mahaifa, kikasance Akullum mai san faranta musu,"    girgiza kanta tafarayi hawaye d'aya nabin d'aya, "    ahankali ta furta ba haka bane,"
Toh menene Jikata?"
Yatambaya Cikin sigar lallashi, "
Girgiza masa kai tayi, Murmushi yayi dan tabbas yasan akwai abunda take boyewa."










To kifad'amun dalili har inde bakyaso nazargeki akan kin yiwa mahaifanki biyayya, "   bansan cutarda wanda yake tareda nine ko kadan banso wani yasake cutuwa kamar yadda najeeb yacutu,"
K'ura mata ido yayi nasan gaskanta abinda yake tinani,"
Cikin hikqma yace kidaukeni matsayin kakanki, danni nadaukeki ajikata kifada mun duk wani abinda yake faruwa da rayuwar ki karki boyemun komai, in sha Allah tare zamu nemo mafita, "
Cikin yarda da tsohon tafara bashi labarin duk wani abinda yafaru har izuwa kwanciyar najeeb a asibiti, dogon numfashi yaja sannan yace mata, jikita tunda naganki nasan kina tareda sihiri ajkin ki saidai baida k'arfii dan atunanina yawan addu'a da kike ya ne yasa abin baiyi karfii ba amma in sha Allahu da addu'a zamu yakesu bbu wani abinda yafi karfin addu'a, " _mutane musani bawai dan kinada damuwa sai jitafi wajen wani yace zai miki aiki awarware sihiri shine masalaha ba A'a akwai addu'oii dayawa acikin qur'anii mai girma wanda su kadai sukan iya samawa dan adam waraka dan Allah mukiyaye zuwa gun wasu malaman yawancinsu bokayene suke k'arya dasunan malamai Allah yakare_





Nasiha yamata sosai sannan yace ga addu'a kiringa karanta ta kartabace abakinki da yardar Allah duk wani mai nufan ki da sharri zai koma kamsa ```waraddal lahul lazina kafaruh bigaizihim lam yanalu khaira wakafal lahul mu'umininal qital wakanal laahu qawuyan azizan hakima```
Wannan addu'a hakika tana maganin sharri dakuma mai nufinka da sharri ahaka yayita mata nasiha sannan yace taje tasamu mahaifanta tabasu hakuri, "
Jikata d'agowa tayi tayi kalleshi, gobe kizo gidana ki kar6i sauran addu'oiin, sannan zansa ayita saukan alqur'anii,"
Sannan abu na karshe bawai danna fito a dangin abadallah ba yakasance yaro mai hankali, duk duniya banda mahaifanki banga wanda zaisoki sama dashi ba, "
Yasoki tun baki mallaki hankalin kankii ba, yasokii tun bakisan kankii ba inatunanin duk wanda zaki aura abayansa yake amma inaso kiyita addu'an zabin alkhairii,"
Allah ya miki albarka amin ta amsa d'an hira suka ta6a sannan yatshi har bakin kofan tarakashi dake yatsufa ahankali yake tafiya sanda suka isah bakin falon taja tatsaya alamu yamata akan tashiga bbu musu tashigo shima yabi bayanta abakin kofa tatsaya ta durqusa guiwaowainta duka biyu sannan ta sunkuyarda kanta, "
Cikin rawar murya ta ce abba dan Allah kuyafemun nayi kuskure amma in sha Allah bazankara maimaita kamarsaba."
Mai martaba ne yayi magana wanda dama tun maganarta tafarko Bata 6ata masa raiba yasan dole da dalili, gashi yanzu yanda tatsuguna tana neman afuwarsu yasa yarinyar k'ara shiga aransa, Cikin sigar gamsuwa yace tashi kice d'iyata baki mana laipyn komai ba Allah yamiki albarka ahankali ta amsa sannan tatshi sum sum tafice, "  mai martaba suka fito sun tsaida zancen su na iyaye kowa ya amince amma sunaso yaran su dai-dai ta kansu, godiya mai martaba yayita musu Ganin haka yakarasa suka tabbatar lallai wannan al'amari nada mahimmancii."





   Karfe hud'u aka fara shirye shiryen d'aukan amarya Motoci ne nagani na fad'a akalla sun kai motoci ashirin kowacce baka ne wulik sunyi parking suna jiran fitowar amaryarsu,"
Itakuwa tana ciki ana mata nasiha sai kuka takeyi, kamar wanda akayiwa mutuwa dakyar aka fita da ita da matanda sukazo daukan amarya mamane riqeda ita suka shiga, "
Fada suka wuce dan anan zata zauna zuwa gobe akaita gidanata,"
 *Hanna* kuwa nad'aki iyakacin hameeda ne tabisu, iya karrama an karramasu, a shashin waziri umar iyayen abubakar aka ajijeta kafin agama biki, shashin yahad'u sosai, site d'in abubakar aka ajiye amare. "
  Sannan wa'yanda suka kawota suka koma gida."






   Karfe kusan 6 labba taga bbu *hanna* bbu dalilin zatajo gashi, bayan magrib za'a fara shirin dinner, "
  D'aukan motanta tayi ta nufi gidan dakyar ta lallashi *hanna* tabiyota dan itada tace bazata ba."
Da'akazo wajen shiryawa ma sanda akayi rikici ce  tace bazatayi kwalliya ba kuma su hud'unsu sanda ummii ta d'auko musu makeup artist,
Sanda suka addabeta ne yasa tayarda aka mata light makeup amma bakaramin kyau tayiba."
  9 aka fara tafiya wajen dinner, su *_hanna_*  sune k'arshen tafiya alokacinda motarsu tatsaya a katafaren hotel d'in alokacin motocin MG suka danno hancinansu Cikin hotel d'in. "








Fitowa sukayi amotan


_ Suka nufi ciki shima MG Fararen kaya yasa manya bakaramin amsarsa su kayi ba gabaki d'aya sai daukan idanuwa yakeyi, "
Amfara gudanar da event kowa yana sha'aninsa banda hanna data takure agefe bayanda ba suya tafita ba amma tak'i."
Shikuwa MG gabaki d'aya ya gundura da zaman wajen gashi ba kalli *hanna* ba kuma andameshi da kallo barin 'yan matan dake wajen, " duk da akayi akwai wasu daga Cikin sojojinsa a wajen amma hakan bai hanashi takura ba,"
Sanda event yakai tsakaiya aka kira k'annen amarya kowa yaje amma banda ita ganin yanda amaryar ta 6ata rai take kollonta yasa ta d'anji bbu dad'ii jakar kud'in tadauko ta nufi gun amaryar liki tafara mata sai alokacin MG yaganta yashagala da kallonta ga wanikyau da tayi sai dai fuskarta akwai alamun damuwa duk sai yaji bbu dad'ii ganin ta Cikin damuwa atunaninsa ko zancen auransa da aka mata ne yassata Cikin wannan damuwar. "






Bata ankaraba sai ji tayi kawai anfara mata ruwan kud'ii na liki kamar itace amaryar."






To be continued


Ur's
   *Z33yb3rw3r*
[12/2, 9:32 AM] Anty Jamila D Ili: *BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

My first novel

 

Page 40


*
   Juyawa tayi dan ganin wayake yimata manni ganin ya jalal yasata sakin murmushimurmushi ahankali tace,"   yaya ina kashiga?"
Bana ganinka, dan ta6e baki yayi, "
Banason hayaniyane yasani barin gidan,"
Sai kun gama bikinku zandawo, "
Harda saleem ko?"
 *Hanna*  tace eh yace mata atakaice,
Sanda yazo dai-dai kunnenta ya rad'a mata kinyi kyau d'an murmushi takarayi, yad'an kama ha6ansa🤔 ya kalleta kamar maisan gano wani abu a tattare da ita amma kinrame kad'an, mai yake damunki? "
Narai narai tayi da fuska alamun batasan tambayan,"
Ganin haka yasashi jan gyalenta ya nufii wata kujera da ita."
Alokacin ran MG inyayi dubu ya6acii har wani hucii yakeyi gashi idanuwansa sunyi jazirr. "
Jiyake kamar yaje ya shaqe jalal,"
Murmushin data masa yatsaya masa arayi gashi yawani ja mata gyalenta ita kuma tabishi. "
Runtse idanuwansa yayi kawai yana fitarda hucii mai tsafii."
Dakyar ya iya fita ya yiwa ango da amaryarsa liki, "
Yana tashi kallo yadawo kansa."
Daga nesa mutane keta d'aukansad'aukansa a photo dan wanda basubasu ta6a kallonsa bama yau sun kalleshi ba'a TV ba, balle masu pics wanda sunsan dasu samu kud'ii kowane mai photographer, burinsa ya d'aukeshi."
Dakyar yatsaya suka d'auki pics da couples d'in amma yahad'e girar sama data k'asa. "
Kusan 12 akagama diner, hanna tace ita dole gidan su zata wuce dakyar labba ta rarrasheta tayarda ta bisu shshin ummii suka nufa lokacin dare yayi sosai yasasu wucewa d'akin labba,"
Wanka suka fara yi sannan suka kwanta. "😴







    Najeeb an sallameshi a asibiti jikinsa yad'anyi sauki saidai damuwace fall arayinsa danko abinci baya iyacii balle magana,"
Iya tambayoyin duniyarnan ammasa amma bbu amsa duk 'yan uwansa hankalinsu yatashi ganin halinda d'an uwansu yake. "
Koda yayansa yakira anty maman amal Bata fad'a masa tasan komai ba saidai tad'an canja muryarta bakaman yadda yasaba jiba sai yabar hakan a hidimar biki."




   Washe gari da safe ko karyawa basuyiba *hanna*  tasa labba dole sanda takaita gida. "
Ahaka tatashi takaita,"
Ummii na falo taga shigowar labba, "
Cikin gajiya tazube akan kujera," 
Ummii ne tace habibty daga ina haka da sassafennan? "
Wallhy ummii *hanna* ce tace saina kaita gida wai zataje tasha magani batajin dad'ii,"
Cikin nuna kulawa da damuwa ummii tace Allah yasauwake, "
Ameen ta amsa atakaice."





K'arfe uku suka fara shirin yin bud'ar kai wanda za'ayishi acikin fada. "
Saikusan 4pm kafin akagama shiryawa,"
Alokacin hanna tadade da isowa Bata wani dad'e awajenba da damu labba tatashi tarakata wajan moddibbo, "
Ba su d'auko lokaciba suka dawo dayake addu'oii kawai suka kar6o,"
Sannan suka juyo. "
Sunsamu angama kawai suka wuce gida hardasu amira," wanda gobe zasu koma, "
Labba ne tasamu ummii adaki akan sallaya ta idarda sallah."
Sannu ummii, "
Yawwa Sannu inakika shiga?"
Naraka *hanna* kun moddibbo ne, "
Murmushin tayi danko sunan *hanna* aka ambata takanji son yarinyar aranta."
Yanzu wajen mai martaba zanje naji zancen yanda suka tsaya akan zancen jiya sunje tambaya, toh tunjiya bamu samu dama munyi zancen canba shiysa yanzu zanje, "
Murmushin fuskar labba ne yafad'ad'a, Allah yasa andace amin tace."
Sannan tamike tayi shashin mai martaba afalo tasamu mai martaba. "
Cikin fara'a da girmamawa tagaidashi,"
Cikin tsolaya tace nabiyo sawu ne, dariya mai martaba yayi sannan yace ohh uwar yaro ba hakuri anaso aji yanda zance yakaya."Murmushin tayi sannan tace  bakasan yanda yaronnan yake zuwa yazaunamin ba Koda bai furta ba amma nagane nufin shi. "
  To ai muntsaida zance da iyayen yarinyar amma munaso yaran su dai-daita kansu yanda abun zaizo Cikin sauki."
To Allah yasanya alkairi aciki da amin ya amsa Suna Cikin zancen saiga MG yashigo da sallama amsawa sukayi sanna yasamu wajen yazauna gaidasu yayi suka amsa masa. "
Zama yayi nan mai martaba ya labarta masa yanda sukayi da mahaifan yarinyar."
Wani irin fad'uwa gabansa yayi danshi yana shakkar tunkararta baisan mai zaifaru ba. "
Murmushin ya kakalo sannan yamusu sallama da godiya yafita."
ya yanke shawarar jibi ya tunkareta dan yasan rana mai mahimmamci ne arayuwarta. "
Da safe su amira da mama suka fara shiri jitaayi duk garin bbu dad'ii daga ita har hameedan, dan da tafiyar da *hanna* za'ayi amma tafasa batason abinda zai had'ata da Najeeb kokadan kuma tasan har inde tatafi zasu iya had'uwa."
Babe yanzu jibi nefa birthday d'ina wednesday amma bazaki zauna ba? "
Srry Beb wallhy mom ce tatakura Nima banso komawaba,"
Badan ransu yasoba su kayi sallama su amira suka tafi, kuma duka bakin sun watse sai d'ai-d'aiku. "
Haka sukaji wani irii bbu amira arannan sunyi bacci sosai, wanda tunda akafara bikin basu sameshiba,"
Washegari sukaje sukayi odering duk wani abunda zasu buk'atq gobe. "





To be continued




Ur's
     _Z33yb3rw3r_
[9/23, 10:28 PM] ‪+234 810 367 2210‬: *BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

My first novel

  _This Page is sencirely dedicated to u my sweetest, cutest amazing, wonderfull, sweet heart *raheenat*  u r such a damsel unique my dear, ILYSM my dear Allah yabar luv 😍 i heart u dear. "_(j'aime ```vraimene mon raheenat vous este un ami comme tout utre) jet'aime ```

Page 41


*
     Sosai suke zurga-zurga dan ganin sun kammala komai kafin gobe, dan gobe da yamma sukesonyin celebrating na birthday d'in a gidan adda hindu,"
Umma takira wanda zasuyi decorating wajen, with pink and white flawer's cottons and balloons."
 Sannan sunyi ordering 2 birthday cakes, pink colour mixing with white da kuma golden colour,"
Sai kuma cup cakes da sukayi ordering. "
Sosai suke tsara yanda komai zai kasance, sunje anwanke mata kai itada hameeda amma batasa relaxer ba,"
Sai sukaje shopping ananne suka sayo kayanda zasu sa. "
Abubuwa basu kammala ba sai karfe tara na dare 9pm sannan suka samu suka gama wasu abubuwan,
Sai alokacin tasamu dama takira labba ta shaida mata,
Fushi tayi bata kirata sunyi komai tareba ce mata tayi akan tayi hakuri taga ta gajii ne da hidiman biki yasa, sallama sukayi ta shaida mata gobe da safe data isoh. "
D'akin ummii ta nufa tasameta da murna ummii gobe fa birthday d'in *hanna* ,"
Cikin fara'a ummii tace To gobe saimu shiga kasuwa amata shopping na gift koh, "
Ummii muje yau mana gobe fa dasafe nakeson zuwa,"
Cikin Murmushin ta tak'ara cewa, yanzufa tara tawuce kibari gobe kinjii, "
Toh kawai ta amsa tafice Badan taso ba,"
Y'an tsirarun mutane aka fad'awa dan basaso suwuce fifteen 15 awajen, "a sunyi yawa sukai twenty 20."
Bacci suka kwanta dan sungaji likis, "
Kusan k'arfe goma taji wayanta na ringing Cikin magagin bacci taduba kawai taga numb d'in najeeb ne kasa picking tayi
Har yakatse,
Can kusan bayan 30 minute akasake kira kawai lokacinma har bacci yak'ara d'aukan, dan kiran farkonma bawai tagama fahimtar mai kiran bane, "
Tura wayan tayi k'asan pillow ba tareba ta duba ba, ahaka har aka d'auki tsawon awa biyu anayi ba'a kira sai bayan 30 minute batareda ta dubaba duka,"
Alokacin da 12 :00 taduba dai-dai lokacin massage yashigo wayan, "
Wanda bata damu ta dubaba,"
Kicin jin bacci tazare wayan tayi switching nata off. "





Najeeb na kwance ad'akinsa yaji yanason jin muryarta haka kawai wanda baisan dalili ba yayi - yayi ya daure ya kasa, shine dalilin d'aga waya ya kirata Koda ya kirata yaga ba'adauka ba yayi kusan 3 miss call ba'a picking yasashi, hakura yakashe wayan gabaki d'aya."



Gajiya ne yasasu makara har kusan k'arfe shida na asuba bbu wanda yatshi acikinsu,
 *Hanna* ce ta d'an bud'e idanuwanta sannan ta mayar ta lumshe, batafi 1 minute da rufe ido ba, sai gata ruff akasa tafado, wanda hakan yasa hameeda mik'ewa zaune bbu shiri tunda taji k'arar faduwa, "
Waige-Waige hameeda tafarayi yayinda ita kuma *hanna* inahh hankalinta nakan neman wayanta da take yi, tunowa da tayi an turo mata massage bata duba ba yasata wannan fad'uwar tanada tabbacin bbu mai turo mata massage awannna lokacin kuma irin wannan rana inba shiba. "
Pillow tad'aga aikuwa saiga wayan tana bud'ewa taga massage ai Cikin ihu tace OMG itz dat numb again," massage tagani Kamar haka,"
*_HBD JAAN ITX TIME."_*
saurin komawa tayi tab'ude na wancan shekaran, " shima dai massage ne kamar haka."
*_HBD JAAN 1YEAR REMAINING. "_*
   Tunanin tazaunayi mai hakan yake nufi da itx tym lokacin menene?"
Ita tasan dai shekaran ta biyar da wannan numb tafara mata massage tun ana 5yrs remain har yadawo itx time to lokacin mene ake irga mata. "
Iya kira tayi kira amma batsamu mai numb d'inba,"
Har campany na layin MTN taje dan tayi bincike anshaida mata cewa layin sai bayan shekara, shekara ake amfanii dashi kuma shi layin ba'a teracging kuma lokacin da aka fad'a mata ana bud'ewa shine lokacin birthday d'inta. "
Zama tayi abakin gado tayi tagumii kawai can kuwa sai maganar captain bala tafad'o mata,"
```Karki damu kin kusan sanin dalilin dayasa muke *bibiyarki*  lokacin   k'alilanne yarage wanda zai amsa miki tamabyoyinki yananan zuwa``` 
Tunani ne fall ranta kamar tayi tagumii kamar wanda aka tsikareta ta tashi aguje tayi hanyar waje, "
Hameeda da take kollonta tun lokacin da take neme neme itama tafita aguje tabita,"
Bata tsaya ba sanda tazo gate sannan ta tsaya alokacin Hameeda ta iso, *hanna*  ina zaki futa? "
Sleeping wears nefa ajikinki."
Bata saurareta ba tabud'e kofar da yake jikin gate d'in, "
Tasakai ta fita, gashi lokacin garii bai wayeba, kodaga sallah ba'adawo ba." To her biggest suprise tana bud'e kofan tacii karo ta qatoton gift a ajiye akofan. "
D'auka kawai tayi ta tsaya duba gefe da gefe bataga kowaba, hakan yasa tajuya, zuwa ciki Hameeda ma tajuya tabita."







Suna shiga daki ta ajiye akan gado tayi toilet danyin alwala, tana Fitowa ta samu Hameeda na jiranta, tsareta tayi ta tambayan *hanna*  waye ya ajiye wannan k'aton gift d'in awaje? "
Murmushi tayi Nima bansaniba abinda nasani kawai duk shekaranda zanyi birthday sai an ajiyemun gift da asubahi a kofar gidanda nake."
Tana fad'in haka tajuya tad'auki sallaya da khimar ta fara sallah. " MG baibar kofar gidanba sanda yaga tafito ta d'auki gift d'in tukunna yatada mota yawuce,"

Bayan da idarda sallah ne tafara duba massage da suka shigo wayanta, Harda massage nasu amira su yaya jalal mutane barkatai,"
Bubbedewa tayi sannan tab'ude Data nanma massages kamar zasu cinyeta rufewa kawai tayi ta kwanta bacci abinta, "
Labba ce tatasheta daga bacci  kusan 9am."
Cikin magagin bacci tace labba har kin iso? "
Eh ke ni ummii nema tatsaidani da tun 7am zan iso,
Babe is ur day wakeup kidena wannan baccin muje musan abinyi, mikewa tayi tashiga bandaki ta yi brush sannan tayi Wanka tafito doguwar riga kawai ta zura ta kalli labba da hameeda sannan tace sai ina?"
Mu ebi drinks mukai gidan anty sai mudawo, "
Ok suka tashi, drinks d'in suka eba a store suka wuce wanda bbu zasubi su saya." basu suka gama zirga - zirga ba sai karfe daya, alokacin 4 za'afara, "
Kuma basu kar6o cake ba."
2 aka gama decorating komai. "
Sanda sukayi la'asar suka fara shiri,"
Makeup artist aka kira tamusu simple makeup saikuma aka yi rolling kai da d'an karamin veil. "
Tayi matukar kyau, gown dinda tasa goldenne sai aka yi rolling da dark pink na veil tayi matuk'ar kyau,"
Sunfara yin abunsu bbu wani hayaniya dan basuyi yawa ba daga saleem dayaki tafiya sai yaya jalal da salman dakuma sauran cousine dinsu anyi birthday party lpy kowa ya gama yatafii 6pm dai-dai suka gama. "
Alokacin labba tadage saisunje gidansu dayake tana Cikin farinciki bbu musu suka wuce,"
Ummii suka samu afalo tana jiransu tana kallonsu tataso ta rungume *hanna*     habibty Allah yak'aro shekaru masu yawa Cikin jin kunya tace amin, dakin labba suka wuce alola sukayi sukayi sallan magrib, nan labba tamatsa ta tatashi tashiga Wanka tashi tayi tashiga bayan tafito ta samu bbu kowa sai wata farar gown mai red flowers mai kyan gaske batada nauyi da mamaki tatsaya kollonta, can sai labba ta bude kofa, au baki saba? "
Mufa munshirya time yana ja, plz get ready,"
Cikin kallon tuhuma tace mai za'ayi? "
Itx a suprise kede kisa kawai."
Bata k'ara magana ba tasa wata yar budurwace tashigo da kit na makeup a hannunta zaunarda ita tayi tafara yi mata makeup, "
Sosai tayi kyau dayake bawani makeup akamata ba."
Tamata rolling da jan veil wani farin kyalle hameeda tashigo dashi a hannunta ta rufewa *hanna*  fuska taja hannunta zuwa mota, "
Labba ne taja motar suka tafi, suna isa akabude motar taja hannunta zuwa wani fili da akamasa decorating da farii da jan ballons kawai ga wuta ta ko ina."
Ta bayanta labba tazaga ta bud'e mata fuska. "
Batasan lokacinda tace OMG, tana fad'in haka tayi wajen tana waige waige tana dubawa." ummii ce tak'araso wajen itada wata wanda kana kallo kusan yar tace afeeya ce. "
Cikin farinciki suka rungume ta suna mata HBD wasu masu aikine suka ringa jerra abubuwa awajen na ciye ciye dana shaye shaye kamarde wanda ake shirinyin proposal awajen."








Wani d'an karamin kit ummii tqmiqa mata sannan tajuya afeeya ma tqmiqa mata itama tajuya labba ne tazo dai-dai kunnenta tace sai kinzo kallon tuhuma tamata Bata samu ta tambayeta ba tayi saurin jan hannun hameeda sukabar wajen,
Wani irin kamshi ne yaringa ziyartar hancinta juyawa da zatayi ta hangi MG sanyeda bakin jeans da jan t-shird gabantane yahau fad'uwa nan take jikinta ya d'auki bari."







To be continued





Ur's
      _Z33yb3rw3r_
[9/23, 10:31 PM] ‪+234 810 367 2210‬: *BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

_Dear Ayusher muh'd ina tayaki murnar kammala buk din ki na zuciya gaskiya buk d'in ya ilimantar Allah yabiyaki kuma Allah yabamu ikon amafana da abinda yake cikinsa. "_
_Ayusher acikin writters dabance basirartama ta dabance zankara fad'a gaskiya zuciya yayi." Allah yak'ara basira da zak'in hannu_  ILYSM


 

Page 42


*
    Kallonsa ta tsaya yi har ya matso kusa da ita."
Wanda hakan yayi sandiyar karuwar buguwan zuciyarta, "
Lumshe idanuwanta tayi ta budesu alokacii d'aya,"
Shikuma anashi wajan tun daga nesa yake kollonta har yamatso kusa dan wani irin kyau yaga tak'ara yimasa."
Juyarda kanta tayi daga kallonsa ta harde hannuwanta a chest dinta. "
Wayarta dake hannu wanta ne tafara ringing,"
D'ago wayar tayi ganin numb d'innna da kusan shekara biyar ana mata massage yasata saurin d'agawa ta kara a kunne, "
Am here" taji an fad'a daga Cikin phone d'in, saurin juyawa tayi dan taji ta yadda maganan ke Fitowa ganin MG tayi sak'ale da waya a kunnensa, "
D'aga mata gira d'aya yayi tayi saurin kauda idanuwanta dan wani irin yanayi taji mai wuyar fasaltuwa."
Juyawa tak'ara yi ta kalleshi Cikin tsiwa tace ko zaka iya fad'amin dalilin tsayuwata anan?."
  Murmushin ya d'an yi sannan yafara magana, "
Nadad'e inajiran wannan ranar, sai Yau Allah yayi zuwanta."
Marairaice murya yayi sannan yace *hanna*  Nadad'e ina sonki nayi dakon sonki na shekara goma, tun kina yar k'aramar yarinya nake sonki har i zuwa yanzu sonki baitaba raguwa araina ba, "
I luv u To the extend that i can't effort loosing u."
I love u then, now an forever. "
Nasan abubuwa dayawa idanna fad'a miki ranki zai bacci,"
Su captain bala way'annan wanda suke *bibiyarki* nine nasasu Am Srry plz don't judge me, duk wani abu nayishi ne dan banason rasakii."
Am Srry if i ever hurt. "
 Wani irin tafarfasa ranta yakeyi dan wani irin haushinsa ne ya turnuketa duk da ganin abin kawai takeyi kamar amafarkii, kuma ita kanta tasan ba dacewa sukayi ba shiyasa bazama ta tsaya yaudarar kanta ba."
Dan ko mahakaho yashafa yajii yasan ba dai-dai ba. "





Tana Cikin tunani kafin ta ankara kawai, sai ganii tayi wajen yad'auki kyalli asaman wajen aka rubuta,"
Will you marry me💍? "
  I promis,,,,, shhhhh ta katseshi."
Kadena yaudarar kanka nima kuma kayaudareni,
Banasonka, natsaneka, kaima kuma nasan basona kakeyiba bazan aurekaba. "
Runtse idanuwansa yayi dan zafin maganganunta."
Zaiyi magana ta k'ara katseshi kaje kasamu wata wanda zaka yaudara baniba, "
Tana fadin haka tafice ta barshi speeceless."
 Waje tafuce alokacin ga dare yayi Bata tunanin zata samu abin hawa haka tayita takawa. "
Tanajin wani irii aranta."
Wani bari na zuciyarta takeji kamar bata kyauta ba, "
Tafiya tacii gaba dayi hankalinta atashe hawayene kebin kowani sako na fuskarta."
   Tunani da yayi Koda tafuta ba'abin hawa zata samu ba,"
Yasashi saurin shiga motar yabi bayanta. "
Can ya hangota tayi nisa bin bayanta ya runga yi yana mata horn amma ko juyawa ba tayi ba,".
Sunyi kusan tafiyar sama da 15 minute ahaka amma tak'i tsayuwa shikuma bazai iya tafiya ya barta awannan wajen ba." d'an tsayawa yayi yaga iya gudun ruwanta." ko ajikinta, taci gaba da tafiya. "
Wasu samari ne su uku dake d'an gaba dasu, suka leqota,
Tashi sukayi daga jikin motanda suke suka fara nufota."
Ja da baya tafara yi dan ganin ita suke nufowa, ganin sun k'ara saurii yasata had'awa da gudu gudu. "


Yareema dake zaune amota yana kallon duk wani abunda yake faruwa, baisan lokacin da murmushi ya kufce masa ba."
Da gudu ta ruga taje ta bude motar tashiga ba tace masa komaiba ta juyadda fuskanta gefe. "
Shima batareda ya k'ara cewa komaiba yaja motan suka tafi."
Akofar gida ya ajiye, sannan yace kije kiyi tunani ta6e baki tayi sannan tace bbu wani tunanin da zanyi shawarace nayanke bazan aureka ba. "
Tana fad'in haka tajuya tashige."








Kai tsaye gida ya nufa Tana shiga ta samu umma afalo da hameeda suna jiranta. "
Koda tashiga d'auke kanta tayi kamar bata gansu ba tayi shashinta."
  Ummace da tun dawowar hameeda ta fad'a mata komai murnace fall aranta jira kawai takeyi *hanna* tadawo ta fad'a mata ta amince, "
  Saurin tsaidata tayi *hanna* ina zakije jiranki fa na tsaya yii."
  Zuwa tayi ta zauna kusa da ita, "
Gani umma, yaya kukayi dashi?"
  Ni gaskiya umma bana sonsa ta fad'a tanaja daga baya. "
Bakya meh?"
Bana sonsa yafada had'eda turo bakinta, "
Ganin umma na shirin buge mata baki yasata saurin rufe bakin."
Haka kika fad'a masa? "
D'aga kanta tayi tana kokarin yin kuka."
Dafe goshinta tayi🤦‍♀ tace ya rabb sa''iidunii. "
Tashi kije bbu musu tamike tayi d'aki da kallon takaicii hameeda tabita."





  Yana shiga gida baizarce ko'ina ba sai d'akin ummii samunta yayi azaune itada labba, "
Ganin yadda yashigo ba fara'a jikinsa duk yayi sanyi yasa ummii sakin Murmushi dama tasan za'a rina."
  Kallonsa da labba tayi sannan tayi murmushi mai ma'anonii da yawa, "
Cikin kwanciyar hankali bbu alamun damuwa afuskarta tace,"
 Ya kukayi da ita? "
Sunkuyarda kai yayi sannan yace tace bata sona,"
Dariya ummii tayi da sanda tafito fili tace, kinja da maganata labba kuma gashi nan kinga zahiri. "
Nasha fad'a miki duk kud'ii da mulkin mutum bakomai ne yake nema yasamu ba,"
Ba ko wace mace bace maisan kud'ii, "
Bakowace mace bane mulki da matsayi yadameta ba."
 Koda na fad'a muku k'inyarda dani kukayi gani kukeyi kamar kud'ii zaisa *hanna* ta amince tanasonka, "
Kallon labba tayi tace ke dakika zauna da *hanna* na 'yan kwanki ni daban zauna da itaba amma ni nafiki fahimtarta,"
Sannan tajuya ta kalli MG tace masa yareema bazaka ta6a samun mata kamar *hanna* ba dan haka duk wani abinda zata maka jurewa zatayi. "
Idan kana neman karin bayani kaje ka tambayi mahaifinka daya yasamu aurena,"
Duk wani abinda zai zame maka alkahairii sai kayi hakuri kafin kasameshi. "



Katashi kajeka,"
Karka hakura sai ka tabbatar kashawo kanta, ita takasance mace kuma yanada kyau ace taja ajinta, dan duk mulki kud'ii da kyawun da namiji hakan bazai hana macen da tasan me akekira ta aji jansa ba, hakan bazai hanata nuna masa kimarta na 'ya mace ba. "
   Kagadai ayanzu haka *hanna*  bud'e baki tayi tace batason dan dana haifa acikina, amma kuma soyayarta bata ragu ko kadan araina ba saima k'aruwa da tasakeyi tasake ninkuwa araina,"
Hakan ya nuna min ita kad'ai ce zataso d'ana tsakani da Allah badan wani abunda yake tattare dashiba. "
Hakan ya nuna min itace wanda zan iya damk'a amanarka a hannunta."
Kada ka karaya kaje inada tabbacii akan zata amince maka Koda kuwa zai d'auki lokaci karka sare. "



Tana fad'in haka tawuce tayi falo jikin labba da MG duk yayi sanyi sosai maganganun ummii suka shigesu,"
  Cikin sanyayyar murya labba tace yaya kadaure in sha Allah nima zan tayaka sai naga burinka yacika. "
Shafa kanta yayi sannan yatshi yafice,"
Labba kuma tafice tayi shashin affan tana nemansa. "






To be continued



Ur's
     *Z33yb3rw3r*
[9/23, 10:54 PM] ‪+234 810 367 2210‬: *BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

My first novel

 

Page 43


*
    D'aki tawuce tana shiga tawuce toilet taje tayi wanka sannan yad'auro al'awala. "
  Sallah tayi sannan ta hau gado ta kwanta, ko jiran hameeda batayiba danjin haushinta take natafiya datayii tabarta awajan MG." bata dad'e ta kwantawa ba hameeda tashigo ko kallon yanda take batayiba ta kwanta."
 Basufii 35:00minute da kwanciya ba wayanta ta fara ringing. "
Dubawa tayi taga unknown, d'an ringing, ganin unknwn numb yasata d'auka dan batasan waye bane." d'auka tayi, tayi shiru tana jiran ayi magana,"
Sanda akafii 2minute kafin akayi magana, "
Sannan sai akace salamu alaikum cikin wani irin husky voice,"   sauri d'aga wayar tayi daga kunnenta yadda muryar ta daketa harcikin jijiyoyin jikinta, "
Kallon wayar tayi sannan tasake mayarwa kunnenta,"
Jitayi ansake magana, "
Are u  there?"
Ka tambaya sai lokacin tagane muryar MG ne saurin datse wayar tayi ta turata k'asan pillow, "
Jin shuru yasashi duba wayan, ganin ankatse ne mamaki yacikashi,"
Shida manyan muatne kekira yana k'in d'auka waishi yau ake kashewa waya. "








Daurewa yayi yasake kira sai can aka d'auka,"
Wai meyene? "
Tafad'a atsiwace, ita kanta sanda abun yamata wani irii dan ita kanta tasan yawucii wulakancii, balle akanta wanda masu aikinsa ma sunfita morewa."
Jikinsane yayi sanyi jin irin tsawarda tamasa. "
K'ank'ance murya tayi cikin sanin tayi ba dai-dai ba tace am sorry i dnt mean to,,,  katseta yayi sannan yace is ok u dnt have too."
Murmushi yakeyi dan yasan ba lallai yacii wuya wajen shawo kanta ba dan ya fahimcii da yarinta take aikii."
 Keh kohh yace,"
D'an turo baki tayi kamar yana kallonta tace nimeh? "
 Kinfiya rigima ne,"
Bai bari tak'ara wata magana ba yace *hanna*   wai shin wani laipy namikine dabakya sona? "
A''iya tunanina na kasance marason magana amma tsakanin d'azu zuwa yanzu maganar da nayi har ciwon kai tasanii."
Tunani tatsaya yi a''iya tunaninta bata gano yanda yamata laipy ba amma kuma baza ta jurii wannan magan ganunsanba dan yana neman karya mata zuciyah. "
   Bacci nakeji, "  kawai tafad'a atakaice."
Kallon wayan yayi yak'ara kllon wayar sannan ya girgiza kaii cikin takaicii sai ayau ya yarda cewa duk mulkin mutum dolene sai mace tajuya shi. "
Batajira yace komaiba ta kashe kiran,"
Tana katsewa, kiran najeeb yashigo kiran kallon wayar tayi kamata d'aga amma batasan famawa kanta wani gurin kawai saita ajiye wayan agefe, "
Sanda ta jira katsewarta sannan ta kashe wayan gabaki d'aya."







Kwaciya tayi ammma sam bacci yakasa d'aukanta, "
Dan haka kawai saita dauro  alwala tayi nafila sannan taci gaba da addu'ooiin da middibbo yabata,"
Sai kusan 2am sannan tasamu bacci yad'auketa. "
Mafarkai tayi kala kala,"
Cikin wani beach ta kalli wani soja zaune da wata mata da yarnsu  wanda suke gina gida ayashin da yake wajen babban yaronne yaturewa k'aramar gininda tayi aikuwa tatshi ta bishi sai zagaye wajen sukeyi,
Tana k'okarin kamoshi,"
Yarinyar na k'ok'arin riqo yayanta ne tafad'ii ak'asa *hanna*  dake wajenne tayi sauri zata k'arasa wajen, ganin baban yarinyar da mamanta sun taso ne yasata tsayawa cakk numfashinta ne yaso d'aukewa sakamakon ganin kanta da tayi da wannan mutumii kuma da alamu matarsa ne. "
Zaro idanuwanta tayi tafara dudduba jikinta ganii tayi ita d'ince kuma ga wata mai kamman ninta awajen sai jujjuya yarinyar takeyi taganii kotajii ciwo saurin jada baya tafarayi tana girgiza kai." Cikin baccinta sai girgiza kai takeyi can kuma saita farka, "
Da addu'a abakinta."


Juyawa gefe da gefe tayi sqnnan tasauke ajiyan zuciya ganin mafarkine ba gaskiya ba, "
Dafe kanta tayi saikuma cann ta ware idanuwanta sakamakon mafarkin da tayi dake dawo mata sai yanzu ta fahimcii wata ganii amafarkinta MG ne," kuma ta tabbata shine tatabayin mafarki dashi wai ya kashe najeeb. "
Alwala takara d'aurowa tanata nafill filii tana neman za6in alkhairii agun Allah ba ita tatashi ba sai k'arfe biyar jin kiran sallan subahii, raka'a taniil fijr tafarayii sannan tagabatar da sallah," tatshi hameeda tayi nata sannan itama ta kwanta bacci ba ita tatashiba sai k'arfe tara. "







Tana kunna wayarta da sakon najeeb na ban hakuri tafara cin karo yana nuna mata baisan maiyasa ya aikata ba kuma baisan dalilin aikata hakan da yayi ba."
Ita harga Allah yanzu kuma tafara sakkowa dan tafajin tausayinsa. "
Tana dubawa kuma taga na MG  mrng text massage."
Rufe wayan tayi duka bbu wanda tamasa replay sannan tawuce toilet tayi brush tafita falo Umma tasamu afalon tana zaune zuwa tayi ta kwanta sannan tayi pillow da cinyar umma. "
Ahankali tace ina kwana umma?"
Shafa kanta tayi sannna tace lpy doughter antashi klau? "
Lpy klau umma",
Tashi kuje kicii abincii kinjii injii umma, "
Toh tace sannan tatashi taje wajen cin abincin."






  Hameeda ganin bbu hali yasata yaskewa, dan fushinta bashi zaisa *hanna* taso wanda bataso ba. "
Haka suka sake sukayita hirarsu,"
MG tun da yaturo mata text d'in safe baisake kirantaba, "
Najeeb kuwa kiransa
Sau uku kenan amma ko sau d'aya bata d'aukaba."
Shikuma anasa wajen MG yak'i kiranta ne dan bayason abunda zai b'qta mata raii,
Yaga kiranta da yakeyi kamar basan hakan takeyiba amma bawai dan bayason jin muryarta ba. "







  Wucewa yazoyi yasamu  labba da affan suna tad'ii, kuma da'alamu bakowa sukeaon yaji ba."
Yana zuwa kusa dasu sukayi shuru kamar muna fukai, "
Kawarda kai yayii kamar begansuu ba."
Ya shige cikin d'akin mai martaba dama afalo suke suke zancen. "
Bayan shigansane najii tanace masa,"
Yaya affan d'an Allah kamatsawa masu rigar nan suyi da sauri kasan  baza muso yaja tym ba, "
To kin tsaida wajeenne?".
Yaa affan wajanda kafad'a akwai kud'ii dayqwa,
 Haba labba kema kinsan money is nit the prob, so yanzu acand'in kawai za'ayi,"
  Barina kira wanda nayi ordering polo shirt awajensu najii ko sun iso, "
Toh tace sannan tatshi tace barina tafii gidansu *hanna*  akwai abunda nakeson yii," maganan rubutun da za'ayi ajiki idanna dawo zamuyi magana, tana fad'in haka tamike, alokacin MG yafito ko kallon yanda suke baiyiba ya wuce dan yaga Alama muna furcii sukeson had'awa,   du lokacinda suka zauna haka to da abuu ak'asa





To be countinued.





Ur's
      *Z33yyb3rw3r*

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

My first novel

 

Page 44


*
    Abaya tabi MG dagudu taratsa tacikin sojojinsa ta kutsa tawuceh har gaban sa taje ta tsaidashi sannan ta tsugunna tana maida numfashii. "
 Shafa gashin kansa yayi sannan yad'an furzarda iska, cikin sanyi yace menene?"
Yaa yareema gudansu *hanna*. "
D'an tsaki yaja ahankali sannan yace ki gaidata yara6a yana shirin wucewa, riqo hannunsa tayi sannan tace yaya dama wani xobbe ne nakeso kazaba,"
Inza6a?"  yatambaya, "
Eh ma *hanna*
Tsaki yad'an k'ara  ja sannan yace wasu irin ring ne?"
Diomond ring, "
  Diamond ring, yayi exclaiming,"  eh tace atakaice to me zatayi dashii? "
 Lokaciin zaizo nidai kawai kaza6a."
Ok muje ciki, shashinsa suka nufa, "
Suka zauna tafara nuna masa,"
Baitsaya bin kyau ba  kawai  yad'auki wanda yafii kowanne tsada. "
Aikuwa readers kumsan basaina 😜."
Fad'a ba kunsan yanda kyawun ring d'in zai kasace." Zaroo ido 😳 hanna tayi, " Yaa yareema kasan kud'insa kuwa?"
D'aga kafad'ansa yayi🤷‍♂ sannan yace,"
Nikuma shii nakeso, kuma kinsan kud'ii badamuwa bane,"
Tashi tayi sannan tace gobe anty hibba zata iso (k'anwar ummii ce) 🤷‍
Yau da daddare jirginsu zai taso, "
Kabani kud'in natura mata,"
Jingina yayi da kujerar sannan yad'aura k'afansa d'aya kan d'aya ya lumshe idanuwansa kamar wanda baisan magana yace kije zantura mata. "
Kallonsa tayi aranta tace kamar bashine mace take wahalarwa ba,"  sai wani shan kamshii yake mata. "
Yaa yareema  akwai abinda nakeson yi da atm dinka d'inne fa tafad'a tana turo bakii."
Miko mata yayi batareda ya bud'e idanuwansa ba, "
K'ar6a tayi sannan ahankali cikin k'unk'uni tace kuma sai nayi abinda naga dama dashi."
Inajinki yace saurii tayi tarufe bakinta tayi waje aguje. "
Mirmushi yayi sannan yace labba kenan."
Tana futa bata tsaya ko'inaba sai gidan su hameeda wucewa tayi ta gaida umma sannan tawuce falo yandasu *hanna*  suke zaune, "
Zuwa tayi itama tazauna sannan tasa hannu agyda soyayya plate dasukeci."
Kallonta sukayi ko ajikinta gabaki d'aya sai wata irin kunyar labba ta lulli6eta tasan koba komai zataji bbu dad'i ace batason yayanta. "
Sake jiki tayi kamar bbu abinda yafaru dan ita batama nunawa hanna tasan amma faruba aamma itakam *hanna*   sai wani sunne kai takeyi,"
Hameedace ganin yanda *hanna*  takeyinyada yasata jan tsaki, juyawa sukayi suka kalleta rai abace tace, "
Kinsan kinada kunya aibazaki aikata abinda kika aikataba."
Kallonta labba tayi taksan ido dan taga reaction d'inta. "
Harara ta wullawa hameeda tace me kuma nayi?"
Ta6e baki hameeda tayi sannan tace ohow gashi yasa kinata sunne kai, "
Tsaki *hanna*  taja daganan bata kara cewa komaiba, itakuwa labba tana jinsu batace musu k'ala ba sai gyadan ta takeci kamar batsan ma sunayi ba."
 Kallonsu tayi sannan tace antyna nazofa arakani nashiga kasuwa ne."   hararan wasa *hanna*  ta gallah mata harara  sannan tace waye kuma antynki."
 Ke mana  aiko kink'ii saina kirakibda anty kuma dole ki amsa. "
 *Hanna*  yaya nasanki sosai wanda inada tabbacin babu wani namiji da zaisoki fiyeda yadda yakesonki,"
Tun ina 'yar shekara goma yake zancenki har izuwa yanzu baitaba daga ido yakallibwata mace da sunan so ba. "
Kuma na tabbata idan ba keba bazqiso wata mace ba kuma bazai ta6a aureba idanba keba." maiyasa bazaki taudayawa wannan bawan Allah ba, shuru tayi ta sunkuyarda kai dan batajin zata iya bata amsa dan haryanzu bata fara son yayanta ba kuma bataji zata faraba."
 Tashi sukayi d'akin umma sukayi suka tambayeta, adawo lpy kawai tace musu, "
Shiryawa sukayi sannan suka saka kai suka fice."
Ashe ba kasuwa dasuje ba gidan afeeyah tawuce dasu wanda ke anguwar taraunii, "
Gidane mai kyan gaske, horn tayi mai gadii yabud'e tashige cikin gidan, bbu wanda yatambayeta wajenda zasuje,"
Tana tsayawa tajuya ta kalli hanna sannnan tace anty muje koh, "
Harara ta 6alla mata sannan tace sunannan bazai futa abakinki bako,"
Fita sukayi suka shige gidan iya tsaruwa gidan ya tsaru  sosai sallama sukayi afeeyah dake zaune afalonta tana bawa d'anta d'an kimanin shekara biyu abincii, sallamraune yasa ta juya sannan ta amsa ganin sune dasauri ta nufesu tana zuwa ta rungume *hanna*  yau yayabtace agidannan? "
Janta tayi zuwa ciki tama manta dasu labba koma ince bata lura dasuba." Muda ba'a damu damu ba saimu koma tunda sharemu kikayi, "
Juyawa anty tayi sai asannan ta  lurada hameeda ruqo mata hannu tayi sannan tajuya takalli labba tace saiki koma toh," au haka kikace? "
To bazan komaba tana fad'in haka tayi ciki tazauna kusa da hanna tazauna,"
Zaunawa anty afeeya tayi kusada *hanna* a kunyace *hanna*  tagaisheta amsawa tayi cikin fara'a sannan tajuya ga hameeda itama suka gaisa cikin fara'a sosai. "
Cikin tsolaya tacewa hameeda, gaskiya kina kama da sis d'ina sosai,"
Hameedane tayi dariya sannan tace aidole, maman mu yaya da kanwa hakama babanmu suma yaya da kanii ne, "
Jijjiga kai anty afeeyah tayi sannan tace gaskiya kam dole ayi kama,"
House girl d'inta ta kira ta sata ta kawo musu abun motsa baki, "
Sosai takejan ta da hira,"
Abin har mamaki yaba labba dan tasn anty afeeya bata kasance daga cikin masu sake fuska ba bata sakan jiki da mutum da sauri amma gashi nan tasake da *hanna*  tabbas *hannace*  tadace da yayansu tasan koda wata ya aura bazasu sota kamar yadda sukeson *hanna* , tabbas son *hanna*  ajininsu yake daga mahaifiyarsu da mahaifinsu zuwa kan uban gayyan MG harzuwa kansu wata irin k'auna sukeyiwa *hanna*  bata misaltuwa,
Haka Allah ya haliccesu  da sonta azuciyoyinsu, "
Sosai anty afeeyah ke hidima dasu kamar. Mai shriin goyonta dan so,"
Hameeda kuwa ganin yanda sukeson hanna yasa acikin ranta tad'au alwashin saita juyarda *hanna*  zuwaga MG dan ba kowane family bane zakace bakasan d'an uwansu kuma suyita lalla6aka ,   jin dad'in irin soyayyar da suke nunawa hanna takeyi dan koba komai tasan 'yar uwarta baza tayi dana sanii ba. "
Sai bayan sunyi sallar azhahar sannan suka fita da niyyar tafiya,"
Anty afeeyah lokacinda sukazo fita rike hannun *hanna* tayi ji takeyi kamar karta futa, "
Ahanyane labba,
Basu wuce ko'iina  ba sai gida."
Koda sukaje sanda labba ta dad'e sosai agidan kafinnan ta tashi tatafi,
Kollon hameeda tayi sannan tace sis mud'anje can muyi magana mana, toh hameeda tace tabita suka je wani waje yanda *hanna* bazata jiyosu ba, "
Sun d'an dade suna magana wanda ni kaina banj mai sukace ba balle *hanna* abinda naji kawai ak'arshe ne hameeda tace in sha Allah haka za'ayi, sai labba tace tam shikenan gobe zan aiko dan bazan samu damar shigowa ba,"
Suna gamawa taje wajan *hanna*  sukayi sallama tatafi bata damuba dan tasan maganarsu bazata wuce itada MG shiyasa aranta kuwa tace zakuyi ku barii mah, "
    Kusan k'arfe goma lokacin *hanna* tagama chttn tana kwance tad'auko wayarta bud'e hoton najeeb tayi tana kallo tana kuka,"
Dan haryanzu tanajin sonsa aranta barin yanzu daya dameta da kira kullum yana bata hakurii, "
Jitakeyi idan bata aureshiba zaata cucii kanta kuma shima ta cuceshi,"
Alokacinne irin soyayyar da 'yan uwan MG ke nuna mata tabbas idan ta ce bazata aureahiba tayi butulcii kuma ta kauce maganar iyayenta kuma gashi ita haryanzu zuciyarta najeeb takeso kamar tayi hauka."
Kuka tafashe dashi mai cike da k'unar rai gawani irin zazzabi dake niyar rufeta, "
Ahaka hameeda tashigo tasameta, zama tayi kusa da ita batama sanii ba saijin muryarta tayi tana cewa,"
Haba *hanna*   wannan wani irin damuwa kikasawa kanki wai? "
Karfa ki manta  cewa kullum da daddare inajin ki kina kuka akan najeeb waishin najeeb d'innan shine autan maza da bazaki iya rabuwa dshiba?"
So kike kisawa kanki ciwon zuciya? "
Toni gaskiya wannan abun ya ishenii zanje nagayawa umma hala ita kiji maganar ta, me najeeb yafi MG da kika za6i najeeb akan MG eyeh?"
   Hasalima bbubabinda yakai MG, yamasa fintinkau yawuceshi nesa ba kusa ba yawu ceshi wucewarda bazai kamoshiba haba *hanna*  maiyasa bazakiso mutumin dayake sonki tun bakisan kanikiba?"
mayyasa bazakiso wanda shine kad'ai zai soki har k'arshen rayuwarsaba?"
 Karki manta bashi yasawa kansa sonkiba kuma kisan cewa zafin da kikeji nasonda kikeyiwa najeeb to baikai kashi d'aya acikin ashirin  daga cikin  wanda MG yake miki ba, "
 Kekuwa wani irin laipy MG yamiki ni natabbata idan akace kifad'a bbu wani uzurinda zaki kawo."
Kiyi tunani kada kije kiyi abinda zaisa kiyi danasani bana fatan hakan arayuwata, "
  Jikin hanna ne yayai sanyi jin magan ganin hameeda,
Juyawabtayibta rungumeta tace hameeda narsa yanda zanyi,"
Ni nasan abin yi inji hameeda, dasauri hanna tad'ago kai tace menen shi? " Sa hannu tayi ta share hawayen dake gangarowa afuskan *hanna* sanda tagama share mata sannan tarike hannuwanta duk biyu ta damqe tace kibani nanda kwana biyu idan baki amince da auran MG ba toh ki yanke ko wani irin shawari,"
 *Hanna* ce tace kwana biyu fa kikace? "
Eh kwana biyu nace wata yar dariyavtayi sannan tace hameeda kina wasa danii nine kike tunanin zaki juya acikin kwana biyu?"
Lallai hameeda haryanzu baki gama sanina ba, "
Nop mu zamu juyaki,"
Keda suwa? "
Kedai tunda kin yarda kawai shikenan nayarda tafad'a batareda damuwa ba dan tasan ba yadda za'ayi ta amince acikin kwana biyu."
Hira suka d'an ta6a sannan suka kwanta. "






Washegari k'arfe sha d'aya sukaje gidan anty samha,"
Dama tunda akayi auren basuje gidanta ba dake rijyar zaki, "
Aikuwa sunsami abubakar agidan sun zauna sukasha hira sosai amma anty samha bataji dad'in yanda taga *hanna* tarame ba,"
Suna zaune su hud'u ana hira anty samh ne takalii *hanna* tace habibty kinrame dayawa meya sameki? "
Hameeda ne tayi saurin kar6e zancen tace anty tsawa kanta damuwar wannan najeeb d'inne,"
Tamke rai anty tayi tace ke wato haryanzu baki fitarda wannan najeeb d'inba ko? "
Abbakar ne yace A'a kyaleta ai ba'ayiwa soyayya haka,"
Hameeda ne tace hmm dan bakasan wanda yake sonta take masa wulakancii bane da sauriii anty samha tace waye? "
Cikin zumud'ii hameeda tace anty wani sojane naji ance duk kasarnan bbu kamarsa kumafa tun ba yanzuba yake sonta tun tana y'ar k'arama itama shaidace akan hakan
Dan gidan sarkii ne ance wai yareemane, yawwa yaa abubakar shinefa yamaka babban aboki, abubakarbsake baki kawai yayi yana kallonta dan ya tabbatar cewa itace *hannan* yareema, "
Zaroo ido😳 anty samha tayi tace badai yareema ba?"
Shidai kuwa inji hameeda, "
Riqe baki anty samha tayi tace aina fad'a miki *hanna* cewa wa'yannan masu *bibiyarki* alkhairine Allah yatabbatar da wannan al'amarii, ba aminba *hanna* tace." hameeda nr tasake cewa kuma baki kalli yanda family dinshi ke sonta kamar zasu cinyeta,"
Abubakar ne yace tabbas yareema na ganin jarabawa dan banta6a tunani akwai wanda yarima zaice yanso yasamu matsalaba, "
Tabbas Allah shine mai d'aurawa bawansa duk wata jarabawa,"
 *Hanna* bawai dan yareema yana d'an uwana ba A'a saidan inason fad'a miki gaskiya Allah yarima  mutum ne wanda samun irinsa yayi wahala,"
Mutim ne daysan darajar dan adam mutum ne mai kare talakawa da dukiyarsu,"
 Idan kika sameshi natabbata kinyi sa'a har karshen rayuwarki, "
Ahqka sukayita bata shawara tashiga tad'ayan kunnen tafita tad'aya sai magrib tukunna abubakar ya maidasu gida."





To  be countinued



Ur's
      _Z33yyb3rw3r_

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

My first novel

 _Wannan shafin nakune yan uwah 'yan nijar, saudat nijar, nafii nijar_halima lawali nijar,"_Kai da duk wasu_yan nijar wannan shafin_ nakune,"
Nagode da_ BIBIYAYAR labarina da kuke yi.
Ina sonku kamar yadda kuke sona_ 😍😘

Page 45

*
    Yau juma' a baba yatashi da zazza6i sosai, "
Hakanne yasa mama takira Abba ta shaida masa."
Baid'auki tsawon lokaciba yashirya dan zuwa duba d'an uwannasa dan umma batamasan da tafiyar ba. "
Sai bayan ya shirya ne yake shaida mata Aikuwa itama tace saita bishi,"
Nan ne yace shikuma bazasuyi tafiya subar yara mata kad'ai agida ba. "
  To ai saisu shirya mutafii,"
To tace sannan taje tafad'awa su *hanna* akan su shirya su tafii bauchi zuwa gobe dasu dawo. "
Basu d'auki ko baba ne ba lpy ba sund'auka kawai tafiyace tataso."
Shiryawa sukayi, "
Sannan umma tace ma Abba ya tuntubii su jalal idandasu wce sai su biyosu abaya,"
Zuwa gobenne bazasu iya zamaba?"
Ai bawai hakan bane dan su dubo babansu ne, "
Ok toh kiramin jalaluddeen d'in, takirashi Abba yashaida masa cewa su sun wuce bauchi duba baba idan zakuje kaida saleem da salman sai ku taho mukam muntafii,"
Toh ya amsawa Abba dashi, sukuma su Abba suka d'auki hanya, "
K'arfe uku tamusu agarin bauchi, direct federal lowcost suka wuce gidan baba dasukaje sun samu jikin nasa da d'an saukii dan haryacii abincii,"
Abba ne yakaishi asitibitin AMSAD nan ake shaida masa kawai zazza6i ne sai asannan hankalin Abba ya kwanta, "
Maganii suka rubuta masa awajen yaje yabiya kud'ii suka koma gida,
Suna komawa yasha maganii,"ya samu bacci kafin magrib daya tashi jikin yayi sauki dan har masallacin sukaje tareda Abba." Aikuwa k'arfe 7 saigasu ya jalal sun iso, "
Kuma bbu wanda suka fad'awa suna hanya,"
Wayar *hanna*   ce tafara ringing tana dubawa taga labba dauka tayi sannan tace,"
Antyna nai takiran wyarki d'azu bata shiga. "
Eh lokacin muna hanya ne,"
Hanyan ina? "
Labba ta tambaya
Bauchi" tace atakaice, "
Cikin k'in gaskanta zance tace bauchi kuma?"
Eh bauchi babane baida lafiya, "
Subhanallah Allah yabashi lpy."
Ameen *hanna*  tace, "
Sannan sukayi sallama."
Labba na tashi bata wuce ko'ina ba sai shashin affan tana zuwa tace yaaa affan *hanna*  tabar garii, "
Garii ya tambaya eh tace ta je bauchi mahaifinta babu lpy,".
Subhanallah yace Sannan yace Allah yabshi lpy da ameen Labba ta amsa, "
Shiru tayi sannan tace ya affan yanzu yaya zamuyi?"
Shine kuma d'azu naje nagama shirya komai. "
Nasan abunyi kinsandai kwana biyu ne kuma gobe kwana biyu zai ciki."
Idan ya cika bamuda wani Excuse dole mudauki na annabawa yin hakan kuma yana nufin saka yaa yareema awani hali, "
Shiru sukayi na 'yan wasu sakanii,
Affan ne yayi Saurin tashi yace i got an idea,"
Wat idea ya affan? "
Mubar komai kawai mu sauka agarin bauchi, zuwa 9am tomorro kowa ya hallara garin bauchi." dat means munyi asarar komai nanan kenan? "
Labba asarar kud'ii kikeji?"
Damuyi asarar damukesonyi yanzu ba gwara munyi asarar komaiba."
Bari kiganii zan kira abdul muyi magana zuwa jimawa nasan zai kama mana kinjii, zomuje wajen yaa yareema. "
Futa sukayi suka nufii shashin MG koda sukajee afalo suka sameshi, yana zauna a lokacin ssau 3 yana kiran layin amma taki dauka daga k'arshe ta danna busy,"
Duk yanda yakeson jin muryarta abinya faskara dan takii d'auka, shigowar su affan ne yasa shi ajiye wayan. "
Waje suka samu suka zauna sannan affan yace yaaa yareema munason army d'inka guda talatin 30,"
Talatin mai zakuyi dasu ya fad'a yana had'e rai, "
 Yayaa idan baka bada way'annan army d'inba kuma kaima ka shirya muyi garin bauchi ba daga gobe," you will loose her forever i mean it forever, "
Kollonsu yayi kallonda fassarashi yakanyi wuya,"
Yaa yareema idan bakasan asamu matsala, duk abinda mukace kar ayi musu, "
Kuje suna Waje sannan zanbasu order, kafin kufita,"
Yana fad'in haka ya lumshe idanuwansa, fita sukayi Aikuwa kafin su fita har yakira yagaya musu,"
Suna zuwa suka za6i sojoji talatin wanda ko wace k'asa sanda suka za6i biyar acikinta, "
Adaren sojojin suka kama hanyar bauchi." Sanda sukaga tashinsa sannan suka k'ara shiga shashinsa lokacin yana shirin fita sallar isha ganinsu yasa yatsaya yana sauraronsu, "
Labba ne tace yaa munaso mudakai gobe da sassafe muwuce bauchi,"
Sai mubi morning flight,
Ok d'aga waya yayi zaiyi kira, "
affan ne yace yaa yareema wazaka kira?"
Zankirane a shiryamun prvt jet ne kafin safiya, "
No yaa yareema it has to be personal idan kayi wannan kiran duk k'asa zata d'auki zuwanka,"
Ko'iina za'a shirya maka tar6a mukuma ba haka mukeso ba, "
Munfiso yakasance zuwan kanka kayii."
Kallon affan yayi sannan yace kana nufin nashigawa, Governor da sarki gari batareda na sanar musu ba? "
Eh yaya labba ta amshe,"
Har inde zakaje amatsayin MG to dole ka sanar amma wannan shigan zaka shigane amatsayin ka na mai neman aure," ba amatsayinka na MG kokuma d'an sarkii ba iyakacii muda kai da zumuje, "
U knw itz imposslbe bana tafiya da sojoji k'asa da goma hakan yana nufin na karya doka kuma kunsan ba abinda natsana kamar in karya doka,"
Ok tom amma yaya zuwa jimawa zumuje muyi booking, "
Ok kuje kuyi nida sojoji 10 hadda Ahmed cikon na gomansu,"
Toh sukace sannaan suka fita danyin booking, "
Zuwa k'arfe taran dare komai ya kammala,"
Sai a sannan yasamu lokacin kiran abdul yana d'aukaa yace ya buddy yakake? "
Lpy klau ya bauchi?"
Bauchi klau,
Sanda suka gama gaisawa yace "
Buddy akwai wani taimako nake nema," Daga d'aya can bangaren abdul yace haba buddy yanzu dan zaka nemi abuu awajena saika kirashi da taimako? "
Ka fad'an mun kawai ina jinka,"
Nan yakoro masa abunda yakeso, "
Can abdul yad'an nisa yace buddy kasan yanayin wajennan fa zaiyi wuya ace ba'asamu wanda yakamashi ba,"
Affan ne yace ka k'o'karta buddy kasan ya yareema ne yakeson wajen, nan ya zayyano masa labari ai alokacin abdul yamike, "
Yace dole ma wannan wajen yasamu barina fita,"
Saikusan 10:30 yqkirashi y shaida masa ansamu wajen, "
Labba ne tayiwa ummii da kanwar ummii bayanin abunda zasujeyi nan tagama Had'a komai sannan taje daki."
K'arfe biyar bayan sunyi sallah suka gama had'a komai,
Nan MG ya shiga yiwa ummii sallama,"
Albarka tasa masa sosai sannaan tamasa addu'a akan Allah yabashi abunda yaje nema,
Zuwa 7am sunsauka garin bauchin yakubu."
A jameel guest palace suka sauka dashi da  sojoji goma da affan da labba idan sunsami abunda sukeso aranar dasu koma"






Kiran hameeda labba tayi bayan tad'aga take tambayanta jikin baba cemata tayi jiki yayi sauki sosai dama zazza6i ne, "
Nan take ce mata sis bamu fasa wannan shirin bafa yanzu gamu mun iso tun safe."
Yanzu yaya kenan sis gashi nabar wannan aikan a kano, "
Cewar hameeda."
Ok yanzu yaya za'ayi? "
Kisameni a jufatu zan wuce sai mu zabo toh tace sannaan sukayi sallama."
Kiran amira tayi tace tazo tarakata bata barii *hanna* taganta ba tafuce suka had'u da amira bata wani tsaya yiwa amira Bayani ba suka wuce jufatu anan suka had'u da labba sukayi sayayyarsu sannaan suka juyo, "
Sun koma gida tasamu anty maryam da anty maman amal sunzo,"
Kiran anty amira tayi sannan tamata bayanin komai, murna acikin anty kamar tazuba ruwa tasha, "
Mama da umma suka kira nan ma aka koro musu bayanii,"
Umma da mamane suka harzuqa wana irin shashanci ne wannan keda labban kukeyi kwana biyu fa kuka bata kuma idan yau bata aminceba kenan kuna nufin ita tacii wannan karan, umma ne ta k'ar6e zancen sannaan tace aiko bata yarda yauba bbu wani kwana biyu a haka ma saita amince, "
Hameeda ne tace ni yanzu ma ba wannan ba akan yanda za'ayi zuwa jimawa taje wajen,"
Zama taje inji umma, "
In sha Allah idan taje duk wani fitina ya k'are ko zuciyar dutsi takeda shi saita amince ayau d'in nan in sha Allah."
Ok toh Allah yayarda Cewar Mama yarinyarda agaban iyayensa ta budii baki tace batasonsa bansa akaba. "
Ni inbanda abun so bama banga mai zanyi da ita ba,"
Yafita komai da komai nesa ba kusa ba. "
Anty maman amal ne tace haba mama wannan wace irin magana ce, koda ace bata kaishi komai ba mace daraja ce da ita kuma ni aganina hakan da take yi kanta take kwatawa yanci."
Yanzu burinmu kawai yau ta amince. "
K'arfe uku na yamma *hanna* tafito awanka sanda tajira aka kira sallah sannaan tayi ta d'an shafe jikinta da turare,"
Wata arniyar arabian gown designer hameeda ta ajiye kusada *hanna* baki da hancii *hanna* tasake tana kallon rigar dan bakaramin kyau tayiba mata ba kai ba ita kadai ba duk wanda ya kalli rigan yasan ya had'u light pink ce rigar kalan da hanna ce mutuwarso, "
Kisa muje anguwa hameeda tace ai abbu musu hanna tasa rigar dan tamata kyau,"
Kai sis a'iina kika saya wannan rigar? "
Tayi masifar kyau,"
Kiyi light makeup mufita kawai hameeda tace bbu musu tayi light makeup daya k'ar6i face dinta, "
Bata bata lokacii ba ta shirya rigar ta matukar karbanta,"
Takalmii hameeda ta ajiye mata farii mai kyau da kuma kuma d'an karamin veil shima fari soll. "
Gyara gashin ta tayi yayi acucii mai kyau,"
Sannan tasa veil d'in tafito kamar wata balarabiya sakk, saidai batada haskensu. "
Amira taganii tace beb yaushe kikazo?"
Yanzu nan taga shigansu irin d'aya da hameeda amma bata kawo komai ba."
  Fita sukayi zasu tafii, a lokacin mama da umma suka kirata, "
Mama ne tace *hanna* kizama mai tausayi rayuwarki, sannan umma tace a kullum kisowa d'an uwanki abunda kikesowa kankii."
Jikintane yayi sunyi nan sukayi musu sallama suka tashi suka fita suna fita hameeda taturawa labba taxt tace mata Suna hanya. "
Ganin sun nufi GRA villa garden yasa *hanna* cewa ke mezamuyi kuma a villa garden?"
Amira madai tambayar dake ranta kenan amma tayi shiru,"
Ke kinfaya saurii ne kitsaya ki gani mana hameeda tace, "
Suna isa alamu yagawadawa hameeda cewa sun iso dan motocii ne awajen dayawa irii daya kuma dukansu marsedeze benz ce," guda daya ce taraba  kala ita farasol ce kodaganan abun zai bada sha'awa, "
Shiga sukayi dama already ansan dazuwansu ba'ataresuba suka shige,"
Tun daga waje waje akafara decorating da pink an white na flawers sai ratsin jaa, "
Hameeda ce tafara ciran matane tana cewa su shiga intagram zata fara daukan live video yanzu,"
Takira matane samada ashirin nan amira taga itamafa baza'a barta abaya ba nan tafara kira itama tana cewa ayi joining. "
Tun daga bakin wajen suka fara shooting live video a insta,"
Dan wajen bakaramin kyau yayiba kan su k'arasa Cikin wajen kowacce tasamu views samada talatin, "
Dan yanda wajen ya tsaru bazaka iya kallo ka wuce ba shi yasa aka fara views nan likes yafara biyowa baya."
Shiga wajen sukayi ainan kallo yakoma sama wani irin kyau waje yayi wanda fad'arsa bata lokacii ne ko shugaban k'asane zaizo wajen iya kacii. " Suna shiga wajen bbu kowa sai flawers da aka jera tako ina, "
Batasan lokacinda tak'arasa Cikin wajena tana k'are masa kallo ba, juyawa takeyi tako ina tana kallo."
Jitayi kamar ana kallonta juyawa tayi kawai taga MG daga nesa yana tsaye ya hard'e hannuwansa yazuba mata ido, "
Ganinsa yasa fara'ar fuskanta yakau ta tamke fuska kamar wanda bata ta6a dariya ba."
Sake hannunsa yayi yafara takowa wajenda take, baya ta rungayi jikuma yana matsota sai jinta tayi kawai ta fad'a a kujera da6as,"
Sanda yamatso kusa sannan ya durqusa akan gwuiwowinsa yace, "
Ina sonki,"    Ina sonki, "
Zanje ko ina na maimaita wannan kalmar zan fad'a alokacinda idamuwana suke arufe kuma zanfad'a alokacinda idamuwana suke abude zan fad'a a yayinda nake bacci," kuma zan fad'a agaban kowa i will tell d hole world dat i love u."
 Inasonki sosai, "
Akanki nafara sanin menene so kuma akanki nakeson k'are so, bana fatan ganin ranar da zan futawa wata mace wannan kalmar ba."
I love u plz marry me  I promise to make u d happiest women on earth. "
 I promise to be honest, to be loyal, to be Your frnd ur brother,
I promise to Luv u forever nd am gonna be the best husband ever,"
Ciro dan karamin kit d'in dake aljihunsa yayi, diamond ring d'inne ya bayyana, sai kyqlli yakeyi, "
Akanki yace,
Will u marry me?"
Shiru tayi tana kallonsa. "
Ranga6ar da kai yayi sannan yace plz marry me."
Girgiza masa kai tayi tatashi tana niyyar fucewa labba ce tayi Saurin k'arasowa wajen, da sauri itama ta zube gwuiwowinta, wanda hakan sanda yasa *hanna* riqe baki ahankali kamar me shirin yin kuka tace "
Labba plz kitashi,
Girgiza kai tayi tace nop am nilling here untill u agreed to marry my brother,"
Hanna plz marry him, "
U'r gonna be the luckies Girl ever,"
An I promise u b d best 6ta inlaw plz👏ta had'e hannayanta, "
Girgiza kai *hanna* tahau yi alamun fa bata amince ba."
  Can kuma su hameeda, sai dabii aketa bugawa a insta, "
 Anty hindu da take Can kano itama sai kallo takeyi ji takeyi kamar ta futo ta wayan ta wankawa *hanna* marii baresu anty samha da bakin Cikin *hanna*  yacikata."
Amirace taqaraso wajen amma bataje dab suba dalilin d'aukanda takeyi, ahankali kamar rad'a tace beb say yes, ya tayi kamar bata jiba kuma sarai tajita,
Affan ne yak'araso wajen gwiwansa d'aya yasa ak'asa yace plz marry him,
I promise to be d best brother inlaw, plz say yes shiru tayi ta tsaya tana kallonsu jikinta yafara yin sanyii, "
Amma fa gaskiya bazata iya ba."
Ana haka captain Ahmad ma ya fito, "
Yasa kafafunsa akasa yace Plz say yes, wasu zafafan hawayene suka fito mata ta runtse idanuwanta,"
Ahaka da d'ai-d'ai sojojin suga runga fitowa sun fito kowanne da wandon kakin soja ajikinsa da jan polo abayan anrubuta, plz say yes da fariin rubutu, sukuwa amira labba da hameeda, jan gown sukasa da bakin d'an kwali. "
 Sai Affan shima jan t-shirt da bakin wandone ajikina."
Wayan labba ne tad'auki k'ara tana dubawa taga taga anty afeeya, a hans free tasa, tana d'auka tace plz say yes dear, "
Aikuwa Can halima takira wayan itama ana d'auka abinda ta fad'a kenan."
Can wayan MG ta d'auka itama yana dubawa yaga ummii d'agawa yayi alokacin tace, "
Ahankali tace habiby tell her dat am gonna be d best n sweet mother inlaw that is hardest to find."
D'agowa yayi ya kalleta alamun taji mai ummii tace. "
Kuka ne yakwace mata dasauri tasa hannuwanta biyu ta rufe bakinta,"
Kamar wanda suka Had'a baki dashi da soldiers d'in, dasu affan da yan Cikin wayoyin sukace, "
Zamu zame miki d best family ever,"
Wayan amira da hameeda ne suka fara ringiing kamar me mutane daban daban sai kira a keyi daga masu cewa ta amince kai kusan duk wanda yakira hakane. "
Hameeda ne tace hava beb say yes mana,"
Runtse idanuwanta tayi sannan ta miqa masa hannunta ttsayawa yayi kallonta,
Labba ce tace *hanna* baki amsa bafa, "
 D'aga kanta tayi ahankali tace na amince,"
Cikin murna yasamat zobben ahannunta data miqo masa, ai yanasa zobben wajen ya d'auki ihu. "





_Yaukam abar *hanna* tasha ruwa danta amince da auren MG_  _z33yyb3rw3r ma tasha ruwa_


_Saura kuma naji nace Page yayi kad'an sai nayi suburbud'a_😜

To be continued




Ur's
    Z33yyb3rw3r
*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )



Page 46


*
   Ihuu badaga mutanen wajanba har wanda suke kallo a insta, sanda sukasa Ihuu."
Hakanne yayi sanadiyar daskarewar najeeb dake zaune ad'akinsa yana riqeda waya ahanunnunsa, "
Tun farkon fara abun yake kallo awayansa,"
Zafii yakejii sosai na amincewar *hanna* dan hakan yana nufin rabuwa da ita dan dolensa yayi hakuri, "
Dan yanda yaga MG daga yanayin kyansa da tsarinsama bazai iya ja dashi ba,"
Balle aje ga matsayinsa, "
Kuka kawai ya fashe dashi na bak'in Cikin rabuwa da *hanna*." hakane ta faru da yaya jalal dan shima Hameeda ta kira shi duk wani abinda yafaru yana watching, "
Tun baiso *hanna* ta amince har yadawo yanajin tausqyin MG kuma har Cikin ransa yakeso *hanna* ta amince da auran MG ko bbu komai yasan cewa MG namata sonda shi baya mata kuma zairiketa tsakani da Allah, zaiso duk wani farin Cikin ta, zai faranta mata fiyeda yanda shi zaimata kuma shi arayuwarsa yanason ganin farincikin ta wanda yanada yakinin zata samu hakan, "
Shiyasa har Cikin ransa yaji dad'in amincewar da tayi duk da cewa yanajin kishi acikin ransa."
Saleem kuwa yana Cikin kallo shida abokanansa farko dayace musu yarsace k'in yarda sukayi, "
Shine yace musu su d'aura bet su halarci wajen hakan yasa, suka nufii wajen a motar baban abokinsu daya d'auko musu dan tafiya yawo."
Ita kuwa anty samha itada Abubakar da suke kallo farinciki kamar zai Kashe su, "
Anty samha ce tace wannan yarinyar taurin kai kamar  'yar aljanu,"
Abubakar ne ya d'aga kafad'a sannan yace amma kinsan ni banga laifinta ba, harara anty samha ta galla masa sannan tace tana wahalarda bawan Allah amma a hakan burgeka tayi? "
Kuma abokinka ma," riqo hannunta yayi sannan yace honey bazaki fahimci halin matane ba,"
Duk wanda yaga ta aureshi Ahaka zaice kud'insa ko mulkinsa ta ganii, "
Amma yin hakan zaisa daniya ta fahimci k'anwar taki ta dabance wani kyqlkyalin duniya duk baida metaa ba."
Kwanciya tayi ajikinsa sannan tace ammadai duk da hakan nidai najii dad'ii ina farinciki, "
Cikin tsolaya yace anya kinkai ni kuwa nifa abokinane kuma cousine d'ina zaiyi aure na tabbata za'ayi bikinda duk fad'in kasarnan ba'a ta6a irinsa,"
Ahaka suma sukayi ta murnar farinciki. "
Ita kuwa adda hindu,"
Tsabar murna lokacin nak'uda ta tashi dama yaya auwal nakusa kawai suka wuce asibiti. "
Ina akabar iyalan gidan sarki kowa na gidan farin ciki idan kacire mutum biyu kilishi da intisar."
Dan bakin ciki kamar zai kashesu intisar sa kilishi tayi agaba tanata rausa Ihuu, "
Ita ai dole sai kilishi tasan yanda tayi ta wargaza wannan aure,"
Kinji na fad'a miki abinda malam yace" yace wannan aure saiya yiwu, "
Amma mubari ayi auren ba za'a rasa abinyi ba kuma kinsan maganar malam daiko har inde yace zaiyyi abu to tabbas zaiyi ki kwatar da hankalinki."
Cikin kuka intisar tace tayaya kikesoo na kwatar da hankalina umma kinsan irin sonda nake masa kuma kinacewa na kwantar da hankalii nayi shiru ya aurii wata ba niba wannan ma ba mai yiwuwa bane, "
Kiduba kiga yanda yazuba gwuiwo winsa ak'asa yana roqarta ta aure shi umma wannan wani irin so yake mata?"
Yabarni insonsa kamar zanyi hauka amma ko kallo ban isheshi ba. "
Kiduba wannan yarinya umma itafa bakyawun arziki ba,"
Kiduba na tabbata da za'a ajiyewa maza dari ita sai 99 sun d'aukeni basu kalleta ba kidubata fa tana fad'in haka takara fashewa da kuka, "
Ita kuwa kilishi sai rarrshinta takeyi dan tafi sonta fiyeda yaranta data haifa acikinta."






Wajen su *hanna*  kuwa celebration aka farayi kai har wanda ba'asan da zamansu bama sun zo wayan dan kallon wayannan masoyan kuma ba'a bari ashiga, "
Sai can su saleem suka iso anan aka k'i barinsu su shiga waya ya d'aga yakira *hanna*  a lokacin ya turo wayarta najikinsa dan idan zaifita saiyabi yad'auke wayarta,"
Juyawa yayi yacewa abokan sa lahhhh na manta ashe phn d'inta najikina."
Kallon mk'aryacii suka fara masa hakanne yasashi kiran hameeda itma bata d'auka dawuri ba sai da yayi 2missed call kafin tadaga, " Tana d'auka yace sis muna waje fa anki bari mushigo ai babu b'ata lokacii hameeda tazo ta shigo dashi hadda abokansa."
 Tun daga nesa *hanna* wanda suke tsaye da labba tafara galla masa harara yana zuwa kusa tace ban wayana, "
Sosa kai yafarayi tace idanka k'ara d'aukamin waya Allah nidakai shi kuma sai ido yake mata akan ta bari abokansa amma takii,"
Sanda ta sulleshi tass sannan tabarshi, "
Amma duk da haka sai wani shan kanshi yake yiwa abokanansa shi ala dole, yarsa zata aurii mai mulki."
Sai gab da magrib sannan sukabar wajan amma har tym d'in hanna bata bari sun Had'a ido da Yareema ba duk yanda yaso ya kebe yayi magana da ita abun ya faskara dan wata irin kunyarsa da kwarjininsane yarufeta."
Sai dab magrib sukabar wajan gida suka nufa, "
Wanda Cikin wajan bbu wanda yasan meyake faruwa jira kawai sukeyi,"
Suna dawowa hameeda tafara zayyana Bayani nan tafara nuna musu, "
Mamane tace kadai anji jiki ace mutum taurin kai kamar maye,"
Umma ne tace kadai tunda ta amince zancen yawuce mana, "



Aranar su labba suka wuce,"   washe gari kuma akatashi da shirye shiryen, kaiwa kayan tambaya. "



   _Plz kuyi hakuri da wannan."_




To be continued




Ur's
 _z33yyb3rw3r_

[9/24, 8:41 AM] ‪+234 810 367 2210‬: *BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )



Page 47


*
  Tun sassafe aka fara shirin zuwa nemo aure, "
Alokacin aka kira baba aka sanar dashi zuwan,
Aikuwa yaje yasamu Abba ya fad'a masa."
Abba ne yace amma yaya gani nayi kamar yayi wuri dasun bari nan da zuwa koda satii ne sai,  "
Suzosu kaga yanzu bawani shiri mukayi ba."
Babane yace nima abinda nagani kenan,  amma idan mukace wani abu zasuga kamar basan abun mukayi ba. "
Kuma ni maganganunda yarinyar nan ta fad'a ranar auren samha sai ina kallo kamar akwai wani abuu ak'asa,"
Kaga kuwa yakamata mu amince musu ayi wannan zancen da wuri kamar yanda suka bukata."
D'an gwauron numfashi Abba yaja sannan yace nima nayi tunanin hakan dan inaga akwai masu yiwa yarinyar nan ba dai-dai ba tunda dakanta tace aidama tasan bazasu barta ba, "
Acika mata burinta kamar yanda ta bukata abarta tazauna haka,"
Ai yaya kanajin wannan magana zakasan da wani abuu ak'asa, "
Kuma ta iya yiwuwa yanzu haka ita yarinyar tajii da kunnenta ne yasa ta fad'ar haka."
Dan ni gaskiya yaya bazan 6oyeba gidankanna bakowa nayarda dashi ba kawai abun yafi yanzu mudage da addu'a sannan kuma musa ayita mana saukar qur'ani, "
Kasan mutum kai baka damu dashi ba amma kai yadamu da rayuwarka."
Baba ne ya nisa sannan yace toh Allah yataimaka sai musan abinyi dan nasan zuwa jimawa zasu iso. "
Shiga Cikin gida sukayi,"
Suka samu mama da umma kud'in aikin da za'ayi na Cikin gida aka basu sannan su Abba suka wuce dan tanadarwa bak'i snacks da kuma drinks, "
  Saleem ne ke fitowa daga dakiin su, Alokacin abokinsa yakirashi dan tun jiya sai samun kira yakeyi,"
Wa'yanda da ba frndz nasa bane, wanda then suna kallo mahaifinsa baida kud'in da zasuyi abota dashi yanzu haka sai kiransa sukeyi,"
Sunaso su jonehh. "
D'aukan wayan yayi cikin gadara."
Daga can Cikin wayan nayi ance palz yadai naji wani labari wai dagaske ne? "
D'an gyarawa yayi yafara koro Bayani yanayi yana wani gadara,"
  Aikuwa duk abinda yake fad'a a kunnen Ammah datake zaune abakin kofa,"
Rikicewa tayi wai metake jine waishin dagaske *hanna* aure zatayi?" kuma dan gidan sarkin kano zata aura?"
kamar yanda tajii Saleem yadad'a, "
Afili tace kai ina haka bamai yiwuwa bane."
Shikuwa Saleem baimasan tanayi ba."
Can garin kano kuwa MG harya gajii da amsa call, dan governor's minister's  ambasador's da president, "
Na k'asa she daban daban sai kiransa sukayi suna mai murna dan abu kamar wasa yabaza duniya sosai,"
Dayawa mutane ke sharing wannan video d'in. "
Aranar kuwa followe'r kamar zasu cinye, amira da hameeda."
Kai har takaiga radio's station, "
Tv chennel's,"
Bana k'asarnan zallah ba har na k'asa she da yawa."
Zance gabki d'aya ya karad'e duniya. "
Kowani tasha kika bud'e labaran kenan." MG daya gajine da recieving call, kawai sai ya yanke call saidai massag gashi har yanzu yan wshing basu barshi ya d'an samu tym yakira *hanna* ba. "
K'anin mai martaba ne zaune a falon mai martaba,"
Magana yake yi, yana cewa, "
Yaya aduba wannan lamari gaskiya baida ce ace ya auri yar gidan talaka ba."
Mahaifin yarinyar fa malamin makaranta ne,"
Kaduba matsayi da dukiya irinna yareema ga mulki, arasa wacce za'a aura masa sai yar gidan malamin makaranta yanzu yaya maiyaci yabawa iyalinsa har za'a gani ayi sha'awar aure? "
Ran mai martaba in yayi dubu yab'aci, dan irin maganganun da k'aninsa yake fad'i ya6ata masa rai,"
Amma dayake dattijo ne mai hakuri yasashi sharewa yabarshi yaci yacigaba da cewa ai wannan yakamata yayi tunda munada 'ya'ya mata sai qhad'ashi da d'aya aciki, "
 Mai martaba ne ya nisa sannan yace,"
Mai dukiya dakuma talaka duk Allah ne yayisu, "
Kuma inaso kasani koda yar bukka yareema yakawo yace yanaso toh ita zan aura masa."
Balle mahaifin yarinyar yanada rufiin asirinsa duk abinda ake nema wajen aure to wannan yarinya da mahaifanta suna dashi addu'a yakamata muyi Allah yasanya alkhairii acikinsa. "
Duk da bahaka yasoba amma jikinsa yayi sanyi." Ammah bata tsaya ko inaba sai gidan kawar ta aminiyarta,"
Hajiya lamii tana zuwa tafara mata birgima tana cewa wallhy malam yacuceni duk kud'in da nake she ace baimin aiki mai kyauba, "
Shege dan iska halama boka ne," 😳nikuwa nace kajimin amman nan dama ke atunaniki wajan malami kike zuwa toka kin yaudarii kankii. "
   Dan wannan ba malamii bane."
  Hajiya lamii ne tayita rarrshinta sannan tace tayi hakuri su k'ara jarrava wani suganii,"
Cikin kuka Ammah tace mai nake dashi dazanje wajan wani kefa kina kallo na tattare duk kada rori na nasayar naba wannan macucin,"
Menake dashi dazan je wani waje,"
Cikin lallashi tace mata kiyi hakurii mutafii wani kauye abincika kinsan irinsu basusan zqfin kud'ii ba sai mu bincika."
Cikin d'an gamsuwa da maganar ta Ammah tayi shiru sannan tace to yanzu yaya zanyi tace kodaiyaya kisan yanda kikayi kika nemo kud'ii koda bbu yawa, "
Gaki da yara ai Had'a musu wuta zakiyi sai sun nemo miki."
Ahaka sukayi sallama Ammah tatafi bayan tagama kitsa mata makircii."

  Can wajen su umma kuwa sunanan suna shiri iya dai-dai gwargwado sunyi k'okari sosai wajan tanadarwa da baki abun buk'ata. "
Alokacinne anty maman amal tace ashirya  *hanna* dan tasan dangin sarauta yanzu haka da mata za'azo kuma zasu bukqcii ganinta,"

Governor na garin bauchi kuwa yasha mamakin ganin cewa MG yasauka agarinsa batare da yasani ba, "
Amma yanzu ankirashi akan cewa jirgin mai martaba yakusa sauka,"
Hakama yakira abokinsa sarkin bauchi yasanar dashi. "
Aikuwa nan ma aka fara shirin tar6an sa."
   Duk ilahiran masu tarban sarkii sun hallara a airpot na Abubakar tafawa balewa."
  Kafin su taso daga kano kuwa sanda zance yakai kunnen fulani kakar MG bakaramin farin ciki tayiba, "
Tunda tajii zancen zuwa tace ai atafar sai anje da ita zataje taga jikanta."
  Dake tana samun kulawa sosai kuma ga kud'ii yasa tsufanta baiyi yawa sosai ba. "
  Aikuwa hakanne tafaru aka shirya hadda gwaggonsu khadija k'anwarsu mai martaba da sauran 'yan uwah zuwa garin bauchin yakubu."
      K'arfe 12 :00  dai-dai jirginsu yasauka a airpot, "
Kai tsaye fada suka wuce,"
  Basu d'auki lokacii ba akayi gidan su *hanna*, "
Alokacin angama shirye komai dan, har Abokan baba samada biyar sun zo tar6an baki da kuma wasu dattijai,"
Yan anguwarsu duk aka had'u, "
Isowarsu ba jama'ar anguwar ba kad'ai har makwabtan anguwar fitowa sukayi dan ganin wa'yannan mutane ak'ofar gidan da suka sauka ne yasa mutane shan mamaki basu k'ara sarewa ba sanda sukaga har Governor awannna tafiyar."
Da fara'a su Abba da sauran dajjijan nan suka fito suka tar6e su Cikin amince, "
Suka wuce falon Abba dasu,"
Su kuma matan Cikin gida suka wuce aka wuce shashin mama dasu,"
Ammah ta window take leqe yayinda wani irin bakin ciki yacika ta har wani dushu dushu take kallo. "
Data sani takeyi marar adadi dabata rabata da najeeb ba da tabarta dashi akan ace ta auri wannan dan banzan mai kud'in." abin bakin ciki ma yanda algaitu ya ciki anguwar tako ina algaita ansan dangin sarauta sun shigo, "gaba ki d'aya anguwar sai ta d'auki kamshii dan duk yanda suka wuce akwai masu bin wajan da turaren wuta na gaushi. haka al'adinsu yake har indai za'aje neman aure a gidan sarauta to anguwar sai tasan da zuwansu."
Jiri ne yafara ebanta Aikuwa awajan ta sulale ak'asa Batasan yanda takeba. "
Gashi hafsat tatafii makarnat rabi'ah kuma tana gidan anty maryam jiya da tazo tare suka tafii."
D'aki aka shiga nan akafara gaigaisawa Cikin mutumta juna."
Nan da nan bada 6ata lokacii ba suka fara abinda yakawosu lokacin an kawo musu kayan motsa baki, "
Alokacin Momy kadija kanwar Abba tatashi tafita sai gata tashigo da dogarawa har guda goma sha biyu kowa da akwatii ahannunsa yashigo dashi ajiyewa sukayi sunayi suna kirari a matar yareema ahaka suka gama suka fice da        baya-baya,"
Kallon kayan suka tsyayi nan aka musu bayanin kan cewa kayan naganii inaso ne. "
  Nan mama tace ai atafar kayan sunyi yawa saidai arage,"
Fulanii ce tace ai matar yareema ta cancanchi fiyeda haka dan haka k'arna k'ara jin wannan abun ai muma yar muce. "
Ahaka sukayi ta hira kamar da ansaba da juna."
Fulani ce tace aishin zaku kawomin kishyata naganta ne kosai nabi duk dakunan ina bincikawa, "
Dariya dukansu sukasa Momy khadija ne tace wa Fulanii,"
Umma wannan kishiyarde ta tsorataki tun daga jinta kika rikice gabaki d'aya saikin ganta. "
Dariya duka d'akin ak'asa sannan Fulanii tace to ba dolena naji kishi ba,"
Tanason kwacemun wannan had'adden miji wanda ni kad'ai keda irinsa. "
Nanma dariya akayi sosai, sannan anty mmn amal tatashi tashiga d'aya daga Cikin d'akunan,"
Can jimawa tafito hannunta riqeda *hanna* kanta rufe da qyale amma fuskanta abud'e yake kanta yana k'asa, "
Tundaga nesa suke kallonta suna masha Allah,"
Dan *hanna*  tayi kyau sosai."
  Zuwa tayi ta zauna acan d'an nesa dasu tafara gidansu ahankali Cikin fara'a suka amshe yayinda Momy khadija taja hannunta zuwa gabanta, "
Tsugunawa tayi ta rungumeta sannan tace welcome to our family dear,"
Hakan kuwa ba karamin dad'ii yayiwa su mama da umma ba sunsan sunakai 'yarsu yanda ake sonta Ahaka kowacce mata tayita rungumeta Cikin farin ciki. "
Daga k' arshe fulani tariqeta gam kamar za'a kwaceta tana cewa aikwa bari mu gaisa ko,"
Aikuwa *hanna* taji dad'ii janta datayi yisukeyi kamar zasu cinyeta dan kowanne acikinsu murna sukeyi sunga matar yareema pics kam alokacin tasha bbu adadii. "
Fulani kam riqeta tayi gam tana cewa Allah yamiki albarka,"
Allah yamiki albarka, abunda take nana tawa kenan hannunta na riqe dana *hanna* duka biyun wanda hakan sanda yayi sanadiyar da yasa *hanna* zubda hawaye. "
Data tuna lokacin da ko mashinshini bata da shi har abin gorii yazama sai gashi waiyau itane Cikin dangin mujinda zata aura suna sonta kamar su halaka."
Fulani ne talura da hawayen ahankali tasa gefen gyalenta ta share mata bata bari kowa yaganii ba ta Girgiza mata kai ko ba'a fad'a ba tasan kukan farin ciki takeyi. "
Dan duk wani labarinta moddibbo yasanr da fulani shi yasa takejin son yarinyarda tausayinta." Maza kuwa suma awajensu sungama yanke shawarar za'ayi aure nan da wata d'aya da satii biyu. "
Ahaka Cikin farin ciki aka gama komai kowa sai yaba halin kowa yakeyi dan daga wajen kowa anga halin karamcii," Daga mata aka futo da huhun goro da caton na mint da dabino, kowane gida abinda ake kaimusu kenan, "
Duk anguwar bbu gidanda baisamu huhun goro da caton d'in mint dana dabino ba kuma,"
Kuma ko ina idan aka shiga sai an shaida musu cewa na neman auren *hanna* ne, "
Duk gidanda aka shiga sai anyi mamaki dan tunda suke sunsan ba'at6a sallama ta cewa anzo wajen *hanna* ba sai gashi yau dogarawa ne ke raba goronta kuma wai hakanma goronda za'akai na neman auren wata shine ake rabashi kowane gida,"
Bayan angama komai suka fito sukasa akira musu matan su tafii. "
  Nan wani bafade yashiga yasanar dasu da suka taso tafiyane fulani ta bud'e gyalen *hanna*ta cusa mata wani d'an karamin akwai sannan aka fita rakasu."

Bqyan sun tafii ne ya auwal yayi waya ya shaida musu tun jiya adda hindu ta haihu, ta haifa d'anta namiji wanda tun jiya yaki fada ne dan bayaso yaraba musu hankali. "




To be continued


Ur's
   *Z33yyb3rw3r*
[9/24, 8:45 AM] ‪+234 810 367 2210‬: *BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

 *Alhamdulillahi am feelling much better,"*
*Thank u all for d du'a, care.* *Massages, luv."*
  *Luv u all* ❤. "


Page 48


*
    Murnane ya 6arke agidan, ga murnar auran *hanna*  ga kuma na haihuwar adda hindu."
  Basu tsaya jan lokacii ba aka shaida masa akan ana sallamarsu su wuce bauchi. "
Dan ga baki d'aya yanzu zaman su zaifii yawa a bauchi tunda shirye shiryen biki za'a fara duk da da d'an sauran lokacii amma kuma yakamata komai afara tanadinsa da wuri."
  Awashe gari kuma abba zai wuce kano,"  domin aikinsa. "
Umma kuma sai anyi suna zata koma."
    Da yamma su adda hindu suka kamo hanya itada yaya auwal, "
Alokacin da su abba sukaji bakaramin fad'a sukayiwa su umma ba."
  Abba ne yana fad'a yana cewa inbanda shashanci yarinya da d'anyan jego zaku d'aukota kuma jegon farko ko wanka bata samu ba. "
  Fad'a sosai abba da baba sukayi,"
Hakuri kawai suke bayarwa dan suma yanzu sun fara danasanin cewa suzo da sukayi ga gari da nisa tsakani tafiyar samada 3hour. "

   K'arfe shida dai-dai hafsa ta dawo daga makaranta,"
Ganin mutane cin cirindo acikin gidansu suna fitowa daga shashin mama. "
 D'akin ammah tawuce nan tasamu ammah afalo a sume da gudu takarasa tana fad'in ammah, ammah, jijjagata tafarayi ganin bata ko motsi yasa tanufi fridge da gudu ta ebo ruwa ta fara yayyafa mata."
Koda ta yayyafa mata wata nauyayyan ajiyar zuciya tasake, "
Can kuma kamar wanda aka zabureta  ta mike tana cewa na shiga uku wallhy boka ka cuceni daka bar yarinyar nan zatayi aure kuma dan gidan sarki Allah ya'isa tsakanina dakai."
Nan tayi shiru tafara dube dube afalon nan idonta yadauka kan hafsat da take binta da kallon tuhuma. "
 Mai Mai ta kalmar tayi tace boka," boka fa kikace ammah? tana magana kuka na k'okarin kwace mata, "
Ammah dama kina zuwa wajen boka dan ya cutar min da 'yar uwa?"
  Cikin in ina ammah tace um um malami nefa fa, "
  Cikin kuka da tsawa hafsa tace ina bambamci ammah har indai zakije wajan wani da sunan ya cutar da d'an uwanka wallhy bokane ba malami ba," Cikin kuka tahad'e hannuwanta biyu👏 ammah na rokeku kudena 6atawa malamai suna idan zaku kirqsu da bokansu yafi, d'an jan numfashi tayi sannan taci gaba da cewa, "
  Ammah nifa *hanna* bawai bana sonta bane karkiyi tunanin bazanji zafin cutarda ita da kikayi ba wallhy ammah dole sai naji zafi dan 'yar uwa tace,"
 Hasalima abinda yasa nakejin haushinta irin yanda baba yake nuna bambamci atsakanine, bayaga haka bbu komai soyayyarta nanan dan k'are azuciyata."
*(gaskiya iyaye yakamata mu kula duk irin soyayya dake tsakanin yara har indai zaka nuna kafison d'aya ko kuma kafi kula da d'aya to jin haushin 'yan uwa zaishiga tsakani dan Allah iyayenmu akiyaye."  nuna bambamci d mahaifin *hanna* *yakeyi tsakani shiyakawo jin haushi tsakaninsu amma bawai dan' d'aya baison d'aya ba dan Allah zank'ara roqon iyayenmu akan mukiyaye hakan idan yayi tsananin har gaba yake haifarwa tsakanin 'yan Uwa)*
Jikin ammah ne yayi sanyi, wani irin nauyin d'iyarta ne ya rufe ta, "
Yarda tahaifa itace ke gaya mata gaskiya."
   Duk ilahirin gidan na tsaye abakin k'ofar ammah duk jikinsu yayi sanyi jin abinda yafaru,"
Shiga ciki sukayi nan idanuwan ammah yafara zuru-zuru kamar wanda tayi k'arya kodayake ai abinda tayi yafii k'arya. "
    Kowanne yasamu wajen yazauna abinda su ammah basu saniba shine tun farkon fara maganar suke tsaye,"
Dan zuwa hafsa ganin mahaifiyarta akwance saita sakee k'ara wanda itakanta batasan lokacinda tayiba hakan yayi sanadiyar janyo hankalin gidan, "
Sun zo shiga sukaji abunda ammah ke fad'a wanda sunada tabbacin idan ta sun shiga bazasuji komai ba yasasu tsayawa."
   Kuka sosai ammah takeyi takasa cewa komai."
 Babane yayi gyaran murya, sannan ya kalli hafsa da kanta ke sunkuye ga baki d'aya kunyar kowa ya rufe ta yace. " Kiyi hakuri d'iyata nasan nayi kuskurenda mafi akasarin iyaye suke aikatawa, "
Ki yafeni bawai dan nafison *hanna* bane yasa haka,"
Dukanku ina sonku kuma 'ya' ya nane kuma inasonku dan haka Kiyi hakuri kicire komai aranki hakan bazata sake faruwa ba da ikon Allah. "
  Cikin muryar kuka tace babana na yafe maka, dukda nima nasan irin biyayyar da *hanna* take maka nima bana maka amma in sha Allah daga yanzu zakazaka sameni me yimaka biyayya."
Allah yamuku albarka baki d'aya aka amsa da amin. "
 Sannan yajuya da kallonsa wajen Ammah yace kin kyautawa rayuwarki,"
Kin cutarda 'yarki Wallhy nayi danasanin aurenki Allah ya wadai irin halinki hak'ika wannan magana tayiwa hafasat zafii amma kuma, Ammah ita tajawa kanta. "
  Sunkuyarda kai tayi Sannan tace dan Allah kuyafeni wallhy son zuciyane yajamin haka,"
Nayi danasani  wannan rayuwa da nad'aukarwa kaina, "
Wai yau yar cikane takemun nasiha ita take gwadamun abunda nakeyi ba dai-dai bane,"
Wayyo Allah na kaicona. "
   Dan Allah kutaimaka ku naima mun gafarar *hanna* bansan dawani ido zan kalleta ba na cutarda ita tuntana jaririya,"
Wallhy har kunyar kallonta nakeyi. "
  Jikin mama ne yayi sanyi tabbas tasan care Ammah ta shiryu dan ita tazauna da ita na kimainin shekaru ashirin da biyar 25 kuma tasan halinta tasan tunda tafara neman gafara to tabbas ta shiryu."
  Dan tunda suke ko yi hakuri bata ta6a ji dai-dai da baba ta ta6a cewa ba. "
  Babane yace gafarar *hanna* zaki nema dan ita kika cutar,"
  Juyawa tayi gun *hanna* gwuiwo winta azube ak'asa tana neman gafarar ta, tana cewa *hanna* nasan na cutar da ke iyakacin cutarwa kiyafeni *hanna* hatta saurayinki da kuka rabu kwanakii ma nice silar rabuwarku ni nasayarda komai na mallaka na rabaku kinga Allah ya nunamin ikon sa kinga irin mijin daya baki. "
  Kukane ya kufcewa *hanna* jin cewa rabata da najeeb akayi har yanzu sonsa bai ragu kokad'an azuciyar taba kuma haryanzu ko d'igon son MG bata fara jiba."


Tashi tayi aguje tabar dakin, wani irin tausayin kanta da najeeb ne yarufeta. "
Kuka tayi iyakar iyawarta dan yanzu abin yadawo mata sabo fill."
  Dakyar umma ta lallasheta tayi sallah, Sannan tashiga tad'aurawa su adda hindu abinda zata samu sucii irin wanda akeso masu jego su sha. "
   Tana zaune ita kad'ai ad'aki hafsat ta shigo, zama tasamu waje tayi Sannan tace *hanna* wato bazaki yafewa mahaifiyata bako,"
Nasan tayi laipy amma yakamata ki yafe mata. "
  Ta nemi gafarki fa."
Ce miki akayi ban yafe mata ba."
  Kin yafe mata ne amma baki gaya mata ba kinsan haryanzu kuka takeyi taki sauraron kowa gani takeyi in baki yafe mata ba, zata shiga wani hali,"
Nisawa tayi Sannan tak'ara cewa *hanna* kinsan yanda d'iya da mahaifiya suke duk laipynda ta aikata bazanso ganinta Cikin tashin hankali ba,"
  *Hanna*  plz kiyafe mata, "
   Hameeda Ce tace *hanna* plz let d bygone be bygone."
  No family is perfect we argue and fight, sometimes we stop talking to each other but *hanna* family is family, luv will alway's be there. "
  Ganin sunason damunta kawai tafuce tabar masu d'akin basu bitava suka zauna ad'akin itada Hameeda."
   Tana futa taga bbu kowa zuruf tashige d'akin Ammah kamar mai tsoron karwani yaganta, "
  Azaune tasamu Ammah nata rusar kuka kamar ranta zai fita har wani dushi dushi take kallo,"
  Zuwa *hanna* tayi tazauna agabanta Sannan tasa hannu tashare mata hawaye, "
   D'agowa tayi tace *hanna*  sa hannu tayi ala66anta tace shiiiishshsh Ammah kidena kuka na yafe miki Allah yayafe mana baki d''aya."
Cikin kuka tace *hanna*  nagode, nagode Allah yamiki albarka, "
Amin *hanna* ta amsa Sannan tace Ammah dan Allah kimin alk'awarin bazaki sake cutarda niba,"
Kar sai na saki jiki dake ki k'ara cutarda ni. "
Ammah bama niba ko wani dan Allah karki k' ara cutarda wani,"
    Girgiza kai Ammah tafayi kuka nak'ara k'ok'arin kwace mata tace *hanna* ki yarda dani na gyara halina wallhy yanzu ko kwaro bana iyajii zan cutar balle kuma d'an adam."
Jijjiga kai *hanna* tayi Sannan tace Ammah ciki abinci dan nasan rabonki da abinci tun da safe, "
Murmushi Ammah tayi tanajin son *hanna* nashiga zuciyarta,"
   To 'yata jeki kawo mana abincin sai muci tare nasan kema bawai kinci bane dariya *hanna* tayi Sannan tace nikam Ammah complex zansha wollah bazanci tuwo ba. "
   Ammah ne tamiqe tace mukam ai saida tuwo, bari kiga nashiga ne eba inyaso sai kishiga ciki akwai complex d'in ." K'arfe tara dai-dai su adda hindu suka isoh gabaki d'aya ta shigata, "
Jin tsayuwar mota yasa *hanna* dake d'akin Ammah mikewa tace su adda hindu sun iso,"
Ammah ne takalleta tace dama tana hanya ne, "
  Eh Ammah yau ta haihu tafad'a ta zumud'i,"
   Haihuwa shine dan rashin hankali zasu kamo hanya. "
  Fita duka sukayi daga bakin hanya Ammah taga duk sunyi laushi daga ita har jaririn,"
Aikuwa nan tajasu sukayi shashinta batareda su mama sunsan da zuwansu na, "
  Bata zauna ba ta kunna heater na toilet d'in tashiga yiwa adda hindu wanka,"
  Sanda tagasata sosai sannan ta koma kan jaririn shima ta wankeshi tass ta nad'eshi. "
Dama kafin ta Fito *hanna* tahad'a mata tea mai kaurin gaske nan danan ta shanye ita kuma *hanna* tayi shashin mama tad'auko farfesunda tayi mata da kawo sata agaba Ammah tayi Sanda taci tasha romo sannan ta kawo mata tuwo dkyar taci tuwon tukunna tasamu k'arfin jikinta, "
Ammah ce tace ta kwanta kafin nan Aikuwa tana kwanciya bacci yayi gaba da ita."




To be continued


Ur's
      *Z33yyb3rw3r*
[9/24, 8:50 AM] ‪+234 810 367 2210‬: *BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r)_

  *Get well soon besty (mom manal)*😭😰."



*Get well soon doughtern besty (action baby)* 😭😰


Page 49


*
    Yaya auwal ne bayan yaje yayi sallan da suke kansa, yafito daga mota ya wuce masallaci dake gidan bbu nisa da masallacin, sannan ya gabatar da sallolin dake kansa sannan yawuce Cikin gida. "
   D'akin mama yawuce kai tsaye, ganinsa yasa mama da umma fara juye juye ko zasuga hindu."
  Ganin yazauna yasa umma kasa hakuri Sanda tace wai ina hindatun? "
  D'an zaro ido yayi sannan yace," umma sun shigo fa tun d'azu da *hanna* . "
Dankwalo umma tamasa tace ungo naka mu abokanan wasan kane?"
Allah umma bawasa bane hadda Ammah ma, su suka shiga da ita, "
  Jin haka yasa hankalinsu kwanciya,"
Amma mamaki ne fall aransu Jin cewa wai a d'akin Ammah take hakanne ya k'ara tabbatar musu da cewa Ammah ta shiryu, "
Kuma suma basusan lokacinda *hanna* ta shiga d'akin ba amma hakan yamusu dad'i dan hakan yana nufin ta yafe mata kenan."
  Basu fita ba dan duba adda hindu dan hausawa ansansu da kawaicii idan sukaje dubata hakan yana nufin Basu yarda da irin riqon da Ammah tamata ba, dukda zuciyoyinsu nasan ganinta Ammah sun daure dan sunsan idan sunyi hakuri zuwa gobe zasu ganta."
   K'ofar *hanna* ta kulle sannan itama ta bi adda hindu suka sha bacci." koda hafsat taji K'ofar akulle kanta tsaye ta koma d'akin mama ta kwanta. "
   K'arfe sha biyu dai-dai, yaron adda hindu yafara kuka tsallara kuka yakeyi bbu ji bbu gani,"
   Ga adda hindu baccinta takeyi batasanma yanayi ba, haka *hanna* tayita rarrashinta dak'yar yakoma bacci. "
  Aikuwa befi 1 hour da kwanciya ba yak'ara tashi nanne Ammah taji kukan ta Fito daga d'akinta ta shigo d'akin."
  K'ar6ansa tayi ta fara lallashi, sai can yayi shiru dan tasan kota tashi hindu bbu abunda zaisamu. "
   Nan yak'ara komawa bacci Ammah ta bada shi ta koma d'akinta."
  Yaro kamar wanda ysan amma tafuta yak'ara farkawa, "
Aranar *hanna*  tasan sunyi haihuwa dan ko baccin kirki batayi ba sai asubahi sannan yaron yasamu bacci."
  Haka Allah yad'aurawa *hanna* son yaron sosai, shiyasa takasa bacci ta kwana reno."
   Sanda tayi sallah sannan ta bi yaron suka kwanta, "
  Ita kuwa adda hindu sassafe Ammah ta had'a mata ruwan wanka ta wanketa,"
  Kollon Ammah tayi tace Ammah in d'aukoshi ne kimasa wankan? ".
   Ammah ne tace A'a kyalesu suyi bacci dan jiya baibari sunyi bacci ba."
   Tausayin *hanna* ne yakama adda hindu da kuma wata soyayarta, dan tasan idan ba d'an uwanka ba bbu wanda zqi maka wannan abun. "
Ga kuma mamakin halin amma daya sauya, dan da ko isasshen kallo basu isheta ba."
Amma tasan wannan amsar sai *hanna*  tafarka. "
   Shiryawa tayi ta karya sannan tafuto ta nufii shashin mama."
Ganinta tsaf bbu alamun gajiya ko yunwa ajinkinta, hakan yasa su mama sunji dad'i."
  Tambayan jaririn mama tayi, tace mata ina yaronne kokuma rowa zaki mana? "
  Dariya tayi sannan tace mama yana nan suna bacci shida *hanna* wai jiya bai barta tayi bacci ba."
   Sai kusan 10 kafinnan yaron yatashi kuma yatashi *hanna* . "
Sai alokacin Ammah tamasa wanka sannan *hanna* ta d'aukoshi suka Fito tareda Ammah suka nufii d'akin mama."
  Zqma sukayi suna hira atsakaninsu hakan kuwa bak'aramin dad'i yamusu ba dan before basu samun wannan had'in kai d'inba. "
   Aranar anan sukaci abincin rana kowa ransa farii kall."
   Koda abba da baba suka samesu ahaka bak'aramin dad'ii sukaji ba, dan sunsan ko bayan ransu yaransu zasu had'a kai. "
   Aranar abba yashirya ya koma shida Yaya jalal dakuma salman."
   K'arfe tara na dare *hanna* nazaune kirqn MG ya shigo dan sai alokacin yasamu dama yakirata. "
   Sanda wayar ta kusan katsewa sannan ta d'auka,"
   Cikin husky voice d'insa yayi mata sallama, "
Sanda ta lumshe ido sannan ta bud'e su,"
Tunda take bata ta6ajin murya mai dad'ii da gard'in nasaba, "
Duk lokacin da yayi magana saitaji muryan har Cikin jikinta."
  Sayya sauk'ar mata da kasala."
Dak'yar ta tataro nutsuwarta, ta Gaisheshi, "
  Amsawa yayi da muryarsa wanda kaman tilastshi akeyi saiyayi magana,"
  D'an tsaki taja aranta sannan a zuciya tace" yafara yiwa mutane magana da kasaita kenan kamar wanda akasashi dole. "
   Abinda bata saniba shine afili tayi maganar."  murmushi yayi wanda saida kumatunsa suka lotsa. " Shiru suka d'anyi na'yan secounds. "
Sannan kaman mai shirin yin kuka tace nifa bakowani irin lokacii nake d'aukan waya ba,"
  Amma kai saika kiranii kuma baka Cemun zaka kiraba, ta k'arashe maganar had'eda murguda baki, kaman wanda yake kallonta. "
  Girgiza kai yayi dan dagajin wannan maganar yasan kawai magana take nema."
    To wani irin sanarwa kikeso nayi? "
  Cikin neman rikici tace ohh hakama zakace?"
  Aisaika kira na d'akin d'in tukunna, "
  Tafad'a tana shirin kashe wayar,
Saurin katseta yayi yace am srry tam idan zan kiraki zan rinqa miki Massages tukunna amma plz karki ki d'aukan wayana."
    Shiru tayi ba tace komai ba sannan yace mata "
  Idan zaki rinqa futa plz kiringa kulawa, karki na fita akoda yaushe."
  Cikin Jin haushin maganarsa tace "
Sai kajira dasauran lokaci kafin kafara bani wannan umarnin,"
Dan gani tayi wannan maganar ya matukar raina tane."
Dafe goshinsa yayi sannan yace, *yah rabb "  sa''iidunii*   bahaka nake nufii ba" 
  Kawai ki kiyaye ne kinsan yanzu sai ahankali mutane kiringa kula daywa ba kowa zaki yarda dashi ba. "
   Cikin halin ko inkula tace To ni tunda bbu wani wanda yacuceni kuma bbu wani mai shirin yin hakan sai yanzu."
  Ganin baxata fahimta ba yasa yaga gwara yayi mata bayani. "
  Cikin murya da kaman wanda kake yiwa k'aramin yaro magana kuma kanaso ya fahimceka yace."
To yanzu intambayeki,? "
  Tace inajii,"
Idan 6ter d'inki tamiki laipy agida me kike mata? "
Kinsan dai ta girmeki baza ki mata rashin kunya ba, kuma baza kice zaki daketaba dan tafii k'arfinki."
Cikin rashin sanin abinda yake nufii tace, wayanta nake 6oyewa. "
Yawwa yace an dalilin dayasa kike 6oye wayanta?"
Mugud'a baki tayi tace waini meyasa kakemun wannan tambayoyinne kamar wata k'aramar yarinya? "
  Srry but ki amsa."
Idan kin amsa zaki zami taki amsar. "
Sabida tanason wayanta," Tafad'a adak'ile. "
Ok tam dalilin da yasa zaki kula kenan dan inasonki,"
  Hmm tace sannan tace sai kace wani d'an siyasa wanda ake neman kashewa zakace wani na kula?."
Cikin ransa yace ya rabb wannan yarinya Allah yad'aura mata taurin kai. "
  Yace eh kusan hakan ne tunda ni soja ne kuma kingani yafi d'an siyasa hatsari,"
Kama ha6anta🤔 tayi sannan tace ehh hakafa, "
Amma ai maganar da kayi kamar akwai wanda suke nemanka ne."
  Ya rabb,, kina fa da surutu yace Cikin gajiya da tambayoyinta, "
Turo baki tayi sannan tace ai bani nace kakirani ba,"
Balle nadameka da surutu, "
Tana fad'in haka d'iff takashe wayarta,"
Murmushi yayi sannan ya Girgiza kai, "
Sannna afili ya furta, Allah ka nunamin rnda yarinyar nan zata daina kashemun waya."
 
  Sanda ta kashe wayan da yan minute wani abu ya fad'o mata. "
  D'aga wayan tayi sannan takira anty samha da saurii,"
Tana picking tace anty bawa yaya abubakar bbu musu ta miqa masa, yasa kar6a ko gaisawa basuyi ba tace, yaya abubakar shine? "
Shinewa?" ya tambayeta? "
Shine?"  takara cewa, "
 *Hanna* ban fahimci me kike nufii ba fa kimun bayani."
Yaa abubakar shine sojan k'asa da k'asa? "
Sauk'arda ajiyar zuciya yayi sannan yace eh shine *hanna*, Aikuwa Sanda gabanta yafad'ii datajii shine." sallama tamasa yace *hanna* wani abinne yafaruu? "
Gyara nutsuwarta tayi sannan tace A'a dama bansani bane nake tambaya,"
Oh ai har hankali na ya kwanta shine, "
Ok sai anjima."
Bazan bawa samhan ba?" yatambaya eh kabarta Kawai saida safe tana fad'in haka ta kashe wayar ta. "
   Tana kashewa ta kira amira tana d'auka tace mata beb, ina wannan mutumin da mukajii ana zancen kasheshi lokacin da mukaje office d'in dady?"
Amira ce tace ehh menene yafaru? "
Kinsan daga baya nace miki naga news an harbeshi."
 Kai beb Kardai haryanzu baki manta da wannan zancen ba, "
A'a ba haka bane beb shine fa,"
Tsaki amira taja sannan tace shine wa? "
Um Um ta tsaya cewa dan ita batasan da sunanda zata kirashiba,"
Dan ko sau d'aya bata ta6a kiran  sunansa ba ita hasalima batasan asalin sunansa ba tajidai labba nacewa yaya yareema. "
  Amira ne tagaji ta jira tace kefa nake sauraro,"
  Cikin saurii kamar wanda takejin shakkan maganar tace shine yayan labba, "
Wani irin ihuu amira ta kwala wanda Sanda *hanna* tacire wayan a kunnenta,"
Ihuu takeyi tanayi tana rawa da murna iya k'arfinta, "
Wanda hakan ba k'aramin kularda *hanna* yayiba ta fad'a mata ta tayata jimami amma ihun murna takeyi."
  Sanda tagama ihunta tace beb mun tafii wallhy. "
  Tsaki amira taja sannan tamayar mata yanda sukayi da MG."
  Itama amiran jikinta ne yayi sanyi tace beb kisa aranki bbu wani abu, in sha Allah bbu mai cutarda ke kinji, nan amira tayita kwantar mata da hankali Sannan sukayi sallama, "
 Haka adda hindu tayita zama a d'akin Ammah ranar suna yaro yacii sunan sa Aliyu, sunansa Kawai yaci amma sai yazo dai-dai da sunan mahaifin Ammah, Aikuwa murna awajenta ba'a tonawa dan iya bajinta tayi bajinta asunan,"
Sosai sunan yayi armashi. "
Anty samha bata samu zuwaba, dan baba ne yahana yace satii biyu kenan da auranta bbu yanda zataje."
Washe gari umma ta koma kano, yaya jalal ne yazo yad'auketa, "
Hameeda kam tace idanta koma To k'afarta k'afar amarya."





To be continued




Ur's

       *Z33yyb3rw3r*
[9/24, 8:59 AM] ‪+234 810 367 2210‬: *BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

_Godiya mai tarin yawa ga masoyana, naji dad'iin addu'oiinku da kuma kula warku, wannan shafin nakune, "  *mamman hassan, mmn waleed, zainab bawa(namesake), maman fodio, mamn khish, jameelah, ayusher ayuba isma'il, Ameena* nagode da kulawarku."_

_Y'an group d'ina inasonku sosai Allah yabar k'auna kuna ssakani nishad'i, BIBIYATA AKEYI 1&2 da kuma QUEEN ZEEYY. Allah yabarmunku zeyybawa takuce."_

Page 50


*
Bayan suna da kwana biyu, Zaune suke ad'aki su shida,suna hira, *hanna* , Hameeda, amira, hafsat, adda hindu, rabi'ah,"
  Amira ne tad'an gyara zama, ta kalli *hanna* tace, ke nifa wajenki nazo, biki sai k'aratowa yakeyi, amma ko zancen anko banji kin fara ba. "
  Ta6e baki *hanna*  tayi sannan tace ni wasu k'awaye nake dasu da har zan wani fidda anko."
Harara adda hindu ta galla mata, sannan tace da'allah tafi kibawa mutane waje, "
 Amira ne tace"   adda wallhy bakiga yanda 'yan matan level d'inmu masu shegen girman kai suke kirana akan idan an fidda anko nakawo masu."
Daa se shegen girman kai ko kallo mutane basu ishesu ba."
Amma yanzu sai wani kirana sukeyi, wato sunsan cewa nice frnd d'inki insasu acikin frnd. "
Dariya Hameeda tayi tace ai wollah ko nice zan yi haka, dariya dukkansu sukasa." "
Adda hindu ne tace wallhy kuncika yarinta da yawa, "
Harara *hanna*  ta galla mata tace wai dame kika girmenine?"
  Wani irin kallo adda hindu ta watsa mata tace"  ke nifa inada yaro. "
 Saidai yaronkan injii rabi'ah,"
  Dan kinsan nidai baki girme niba. "
  Yakamata dai kufara bani girma danni yanzu na wuce sa'ar ku." inji adda hindu,
 Hafsat ce tace nikam dan Allah kubar wannan abun yanzu musan abinyi,"
  Dan gaskiyar amira ne yaci ace yanzu munfara shirye shirye. "
  Ana cikin haka Massages ya shigo wayan tana dubawa taga MG ne."
  Anrubuta zankiraki 8pm plz pick it. "
  D'an siririn tsaki taja wanda yaja hankalin Hameeda ta kai kallonta kan screen na phone d'in,"
Rike baki tayi tahau salati, yanzu ke *hanna* idan zae kiraki Sayya nemi izini? "
 Ina ruwanki bansan munafurcii," inji *hanna*
   Rabi'ah ne tace kyaji dashi anaso ana kaiwa kasuwa."
Idan ba haka ba waye zai samu mijinda samunsa na wahala kuma kice bakyaso inbanda gulma. "
   nifa kun fara isata inji *hanna* idannace bana sonsa ina ruwanku?" ai ba'aso dole."
Hameeda ne tace ku rabu da ita duk munafurcii ne."
Allah adda baku ga ranarda muka fara had'uwa dashiba dan ya tsaya yimun magana shinefa ranta yabacii ta koma Cikin gidanki da b'acin rai. "
  Kuma idan ba haka ba gata ku tambayeta,"
 *Hanna* ganin batada na cewa yasata yin shiru da suka isheta ta fice tabar musu d'akin."


  Ummii ce zaune a falonta, itada afeeya da anty hibba da kuma afeeya,"
 Shirye shiryen zuwa had'o kayan lefe sukeyi, jibi zasu tafii Yayinda intisar kuma nanan wani irin zazza6i ne yarufeta, har kullum wani irin son MG ne yake rufeta wanda, tarasa yanda zatayi duk wani hanya dazata bi wajan nuna masa tana sonsa abun ya faskara dan baimasan tanayi ba."
  Yana chan yana son maso wani kamar yanda itama intisar takeyi,
 Koda affan yaji mai yake damunta hakuri kawai yabata dan ya tabbata cewa yayansa yayi nisa baijin kira, "
 Dan irin sonda MG ke yiwa *hanna* Koda ta aureshi wahala kawai zatasha,"
Da haka yayita bata hakuri sannan yace har in dai mijin kine to bbu makawa sai kin aureshi, komin dad'ewa, dan yayi aure hakan bawai yana nufin bazai k'ara wani ba kenan."
  yayi mata haka ne kawai dan kokad'an baison intisar ta aurii MG dan aganinsa kokad'an basu dace ba."
 Kamar yanda yakejin intisar amatsayin yar uwa haka yakejin *hanna* bazaiso ko d'aya ta cutu acikinsu ba,"
  Da haka intisar tasamu ta warware, dan yanzu tasa aranta ko bayan auren saita samu hanyar da tayi ya aureta."


    K'arfe takwas dai-dai, MG yakira *hanna," yana kwance akan bed da pillow a chest din sa ya matsae pillow d'in sannan yaa k'urawa fan ido, jiran kawai tayi picking yakeyi,"
Sanda takusan katsewa kafin ta d'aga,
Sallama tayi ciki-ciki,"
Jin muryarta haka ya saukar masa da kasala dakyar ya iya amsa sallamr. "
Itama lumshe idanuwa tayi sakamakon yanda muryar ta daki dodon kumnuwanta,"
Duk yanda takejin rashin sonsa aranta amma fa ba k'arya itama tasan komai nasa yayi saidai kawai tak'i fad'a. "
Cikin ranta kuwa ji takeyi kamar bata ta6ajin muryar ta takai tasa dad'ii da gard'ii ba."
  Jin shiru yasa shi tunanin kota ajiye wayanne, "
Are u there? Yayi questioning Cikin whisper voice, umm kawai ta amsa Jin irin muryar da yake magana da ita wanda take hanata aikata komai."
   Kin wunii lpy?"
Ya tambaya, sai sannan taji kunyar gaidashi , "
  Ina wuni tace sannan yayi 'yar dariya kafin ya amsa,"
  Turo bakii tayi sannan tace kai ko?"
Dafe goshinsa yayi yace owwh Allah nime? "
 Sai kayi ta yiwa mutane dariya tafad'a had'eda twisting lips d'inta kamar wanda yake kallonta."
  Inbar dariyan? "
Yatambaya eh tace kanta tsaye Eh"
 Siririn murmushi yayi sannan yace to ai bama kowa nakeyiwa ba."
Umm kawai taqara cewa,"
  Zuciyarta ne keson masa tambaya duk lokacin da yakirata amma saita kasa."
Daurewa tayi tace masa, in tambayeka mana? "
 Ehem inajii yace,"
Cire wayan tayi ta harareta sannan ta kwaikwayi irin maganarsa, "
Yana yiwautane magana cikin gadara, mtsew."
Yaushe ta ta6a kallona lokacin da kace in yarinya kuma a'iina? "
  Yi yayi kamar baiji mai tace ba yace, gobe  ina hanya, takaicine yacikata nak'in amsa mata tambayarta tace ni karkazo."
  Baisan lokacin da yatashi zaune ba ya waro eye's dinsa yayinda eyeballs d'insa masu shape na oval suka k'ara girma, yace karfa inzo kikace? "
Eh ta amsa atakaice,"
  To idan banzo ba yaya zamuyi mu tsara yanda event's dasu kasance? "
 Ni basai anyi event ba,"
  Siririn murmushi yayi wanda sanda both side na dumfull nashi suka lotsa."
 Sannan yace nifa naga alamu har yanzu akwai yarinta mai tarin yawa ajikin ki, "
Ranta ne ya6aci jin kiranta da yarinya da yayi, kamar zatayi kuka tace nidai wallhy kadena cemun yarinya,"
  Rufe bakinsa yayi sannan yace nadaina,"
  Fusata tayi jin abin kamar zolaya ma yazama masa tace kaid'in dame ka girmeni? "
 Duk irin dakiyarsa da rashin son yin dariya amma baisan lokacin da ta kwace masa ba yahau yinta kuwa bbu kakkautawa,"
Jin ya maida ita mahaukaciya yasata kashe wayar, sannan ta kifa kanta a fillow tasha kukanta ta koshi. "
Batabi takan zancen zuwansa ba ta kwanta tayi baccin ta koda safe ma tanayin sallah ta koma bacci, sai 9 tatashi, bayan tatashi ne tatuno da zancen zuwansa, ta6e baki tayi tace ai tun da nace banso yazo halama yafasa, haka tacii gaba da damuwowinta."
   Kusan 10 taji shigowar sako wayarta, "
Dubawa tayi taga MG ne, an rubuta in sha Allalh zuwa 1 zamu sauka."
Rasa yanda zatayi tayi, idan taje tafad'awa mama dole zata mata fad'a. "
Shiga kitchen tayi yanda amma ke zaune ta inna kaltu suna aiki,"
Ra6e-Ra6e tafarayi kaman munafuka, "
Ammah ne tajuyo tace"   *hanna* meyafaru? "
Sosa kanta um um tafara cewa, kallonta Ammah ta tsaya kawai,"
Ummm dama wai zaizo ne k'arfe d'aya, Ammah ne tace waye zaizo? "
 *Hanna* tace shii man, 6ata rai Ammah tayi tace ke banason shashancii shii wah?"
  Ammah yareema "
Yareema?" Ammah ta maimaita zaizo yau? "
  D'aga kai *hanna* tayi,
Tun yaushe yace miki yana zuwa?"
Ammah tatambaya, kamar wanda take tsoron kar Ammah takai mata duka sai wani kakkare kanta takeyi da hannuwanta tana Sosa kai tace tun jiya, "
Salati Ammah tayi ta sanar da ubangiji wanda haka yafuto da mama dake d'aki tana tambayar maiya faru?"
Ammah bata tsaya bata amsa ba tace lallai 'yarnan kin cika marar kunya, wato ke ba' aisa afad'a miki magana bako? "
Yanzu da kike fad'amun k'arfe goma da rabi mai kike tunani zanyi kenan?"
  Aikuwa ke yanzu zaki Shiga kasuwa kuma kidawo da wuri azo ad'aura musu abincii shashasha kawai, mama ganin basu gayya cetaa ba cikin maganar yasa taja kafafuwanta ta koma. "
 Kud'i Ammah tabata suka Shiga kasuwa itada hameeda da hafsat, duk wani abunda zasu buk'ata sun sayo, suna dawowa suka hau yin aiki batareda su Ammah sunsa musu hannu ba dan sun iya komai nasu."
Dake aikin ba mutum d'aya bane 1 dai-dai suka gama aiki,, su MG kuwa dake sun d'an samu delay sai lokacin jirginsu ya tashi, dake tsakanin bauchi da kano ba wani nisa bane yasa basu jimaba suka sauka masallaci suka nufa sukayi sallah dashi da wayanda suka rakoshi, yaso tafowa shi kad'ai amma hakan bamai yiwuwa bane, "
Baisanar da zuwansa ba amma duk da haka sanda yasamu wanda sukazo tar6ansa ciki kuwa harda governor,"
A government house suka yada zango, a lokacin kuma hanna ta Shiga wanka aka gyra falon baba yayi kyau banda kamshi bbu abinda falon yakeyi, wanka tafito ta sanya jan swiss d'in da anty maman amal ta d'inka mata tunda tasa agidanta sau d'aya bata k'ara sawaba,"
Shi tad'auko tasaka yamata kyau sosai, sannan tad'auki bak'in mayafii. " Light makeup tayi tabi duk jikinta da humra mai dad'ii, "
Nikuwa nace *hanna* ana ba'aso amma irin wannan kwalliya haka🤔🤷‍♀
Sai pass 2 kafin suka iso gidan, falo saleem yakaisu, sannan ya fita yabasu waje sucii abincii, captain Ahmad ne ya mtso kusada wermer's d'in yace bari mufara cin abinciin amarya tun daga yanzu, harara MG ya dalla masa, "
Haka suka zauna sukacii abincinn MG kuwa kokad'an bai ta6a ba."
Shida yaransa guda tara sukazo shi cikon na goma, "
Shida captain Ahmad da captain bala da wani wanda bansan ko waye bane sukasa jamfa yayinda sauran kuma duka kakii ne ajikinsu,"
Captain bala da wasu sauran uku ne kawai fatansu yad'anyi duhu suma ahakan sunada haske agaban sauranne fatarsu tayi duhu dan su d'in sauran ba blacks bane. "
Danna wayarsa yayi yak'ira *hanna* a lokacin amira ta iso tare suka tashi suka nufii d'akin da su hud'u da amira hafsat hameeda da *hanna* da sallama suka Shiga lokacin sun gama har sun gyara wajan, gaisawa sukayi sannan su amira suka mike da niyyar futa, "
Wannan d'aya wanda yasa jamfa d'innan wanda tare sukayita bibiyar *hanna* da captain bala ne yak'urawa hafsat ido har suka fice ainihin kama suka masa da *hanna*   sai bayan sun fita ne sauran sojojin suka fara gaisheta, amsawa tayi amma da captain bala da kuma wannan d'ayan suka gaidata kin amsawa tayi tabisu da harara, ".
Wanda su kansu basai anfad'a ba sunsan ma'anar hararar yayinda MG ya riqe dariyarsa,"
D'ayanne wanda bansan sunansa ba yace yalla6ai anema mana afuwa tuba mukeyi. "
Kollonta MG yayi bqice komai ba."
Sosa kai captain bala yayi yace ayi hakuri madam, "
Kawarda kanta tayi batace komai ba,"
MG ne aransa yace yar rigima, "
Gyara zama yayi sannan yayi gyaran murya, lokacii d'aya dukansu suka tashi suka fice yazamana daga ita saishi,"
Turo baki tayi tace ina wuni, lpy ya amsa atqkaice nan suka gaisa, yace yau zamu koma nazone naji shirye shiryen da zamuyi ta6e baki tayi tace nifa bzanyi wani shirye shirye ba. "
Karkace kansa yayi yace waii dama da gaske kikeyi?"
D'aga masa kai kawai, baisake cewa komai ba yace ban phone d'inki bbu musu ta mika masa,"
Numb d'in amira da hameeda yayi dialing yace suzo ba 6ata lokacii suka zo su uku, sannan ya kira captain Ahmad yace yazo shida c bala da kuma c bilal, ba 6ata lokacii suka Shigo nan suka fara shiri kamar wasu sune amaren sosai suke shiri saikace auran y'ar shugaban k'asa, sake baki kawai *hanna* tayi tana kallonsu sanda, suka gama sannan MG yace yanaso ya gaisa dasu mama, saleem ne yamasa iso har ciki yashiga ya gaidasu,
Suna gamawa ya damqawa amira atm sannan suka wuce. "


   _Idan kunga mistake afuwan bansamu lokacii gyara ba."_



Comment



To be countinued




Ur's
      Z33yyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

_*Y'ar uwa, Y'ar uwa Y'ar uwa, kalmar nan tamkar zinare take, agaskiya ina alfaharii dake Y'ar uwata my other half, antyna ba na wata ba,"*_
*Anty rashida wannan shafin nakine durungum ke d'aya ina sonki ina alfaharii dake.*



Page 51


*
    Shirye shiryen bikine yafara kankama daga kowanne bangare,"
Kokad'an yanzu su *hanna* bbu zama yau Suna chan gobe Suna chan, "
Koda ita bamai yawan k'awaye bane amma tanashan mamakin irin mutanen da amira ke gayyata takeyi,"
Acikin week d'in hameeda tatafi kano dan itama akwai abunda takeso tayi acahn d'in, kuma baza'a rasa mutanen da zata gayyata ba. "
Acikin satin su amira da *hanna* akayi resuming skull,"
Alokacin abubuwa sukayi musu zafii,
Yanda abun yazo dasauki ma dake IT zasu tafii, "
Kuma *hanna* komai na IT d'inta agarin bauchi tacika,"
A accnt d'in da yabada atm su amira suka cire kud'ii mai yawan gaske, aka fidda anko masu kyau da tsada,"
Kala uku-uku, kowacce k'awa aika mata da nata akayi,"
Aikuwa murna wajen k'awayen ba'a tonawa, "
Sai satiin biki za'a kawo lefe,"
Ana biki sauran satii biyu, "
Kawai ranar saiga ummii ta aiko larabawa guda biyu masu gyaran jiki,"
Abun yabawa su mama da Ammah mamaki, "  Dan aganinsu su yakamata su nemi mai gyara musu yarinya sai ga, mahaifiyar ango nan taturo,"
Ba'ad'auki tsawon lokacii ba aka ware musu d'aki ashashin Ammah, "
Nan da nan suka fara gyarata ba'a barin kowa yashiga ganinta ko MG ma sun hanata d'aukan wayqrsa duk yanda yaso kiranta akashe kullum wayanta, abun ba k'aramun damunsa yayi ba," yaso yazo amma shima nashi hidin dumin ya masa yawa, "
Har IV na bikin su amira ne suke rabawa hameeda ta dawo tare suke fita,"
Idan sunfita tun 11 basu dawowa sai dap magrib, "
Yanzu gabaki d'aya amira ta dawo gidansu *hanna* dazama,"
Dayake aabubuwa sunyi yawa,"
Cikin kwana biyar *hanna* tadawo itada larabawan babbancin kad'anne dan bakaramin kyau tayiba, "
Dakyar su amira ke samun ganinta sau biyu ko uku arana, da abin yafara yawa suka nemii mama ta acanja musu gida,"
Da farko mama tak'ii amma daga baya umma da amma suka ce su kansu amaren zasufii sakewa, har indai suka samu privacy, "
Gidan Anty maman amal suka koma dayake ita ma ta koma gida tun da bikin ya matso kuma mijinta yayi tafiya,"
Sosai sukaji dad'in gidan dan yanzu Suna d'an samun sakewa, ita kanta *hanna* yanzu tafijin dad'i Suna tareda su amira yanzu ana barinsu su zauna waje d'aya tunda gidan a Rufe yake,"
Ko abu *hanna* taruqe sai yayi sassanyar kamshinda takeyi balle wajanda ta zauna, ko tawuce, "
Itada hafsat hameeda amira ne sai hafsat da kuma way'annan larabawan,"
Abida da Aisha, "
D'aya matar tad'an manyanta d'aya kuma matashiyace dabazata wuce shekaru 30 ba."
Sa'ii Sa'ii umma na mata aika. "

Su labba kuwa iyayen biki ko ganuwa ba'ayi duk wani hidin dimu itace akan gaba,
Hatta anko da suka cire ma sanda suka tura mata taganii sannan suka fitar." da hameeda zata tafii sai tatafii mata dashi. "
Suma chan sunyi nasu anko dun,"
Duk da cewa nasu classical ne, "
Dan swiss k'arshen tsada sukayi order d'insa,"
Suna son sufita daban Suna shiga agane cewa dangin ango sunzo wannan na ranar diner kenan, "
Sauran ranakun kuwa shirin da sukayi saisu Kansu dan bamai fad'uwa bane."
Idan kaga intisar zakaceq ba ita bane,"
Dan ta kwantarda hankalinta, kokad'an yanzu bbu damuwar komai atattare da ita, "
TA ware abunta shiirye shiryen biki kawai takeyi, itama barnarda kud'ii takeyi wajen bikin, kilishi har mamakinta takeyi,"
Hakanne yasa takirata d'aki zaunarda ita tayi ta dafa kafad'unta, sannan tace"
Intee kin daina son yareema ne?? "
Girgiza kai tayi tace haba umma ya kike wannan zancen kinsan bazan ta6a daina sonsa ba."
Kilishi ne ta nisa sannan tace mai hakan yake nufii kenan? "
Kinfasa burinki na auransa?"
Nan ma Girgiza kai tayi tace wallhy umma ina nan akan baka na, bazan ta6a hutawa ba harsaina aureshi. "
Nisawa umma tak'arayi tace tom wannan wani irin rawar k'afa kikeyi a auransa?"
Intisar ne tace oh umma duk way'annan tambayoyi  ki ajiyesu amsosunsu sunqnan zuwa. "
Tana fad'in haka tatashi tafice tabar kilishi da zullumi Tunani takeyi to menene yasa ta farin ciki haka bayan tana sonsa?"
Haka dai kawai tayi hakuri da way'annan tambayoyi. "
Gashi wani k'arin abun haushin ma bai wuce yanda 'ya'yanta suke narkarda naira akan wannan bikin ba."
Da intisar taso ya aura. "


  *Ina labarinn najeeb*
====
Najeeb tun lokacin dayaga *hanna* ta amince da auran MG yazama k'aramin mahaukacii yabar suma tayi wani buzu buzu a kullum da ciwon son *hanna* yake kwana a kullum yatuna abun da yamata laifin kansa yake kallo,".
Yayi kuka har yagajii kamar ba babban saurayi ba ya fawwalawa Allah komai, dan yanzu magana ma wahala take masa,"
Kokad'an bai shiga harkokin jama'a yafii ganewa kullum yana d'akii dan yanzu ya tabbatar *hanna* tamasa nisa, "

MG ga baki d'aya yau yanajin sa kamar me, yatashi da sonjin muryar *hanna* Gashi ya kira wayarta a kashe."
Massage yashiga rubutawa kamar duk wani lokacin da ya kira yaji wayan akashe sai yatura massage, "
Massages d'insa sunfii ak'irga acikin wayar amma ita batsanma ya turo ba."
 *Hanna* ce zaune afalo su hameeda sun fita, itakuma zaman kad'aici ya isheta, kawai ta tsuncii kanta da son kunna wayarta, "
Jakarta ta nufa ta d'auko wayan, tayi plugging din cherger sannan ta kunna wayan, sanda tagama ta kunnu tafara kallon Massages d'in MG atake tajii wani tausayinsa yakamata,"
Danna numb d'insa tayi zata kira, haryana shaurin yin ringing tayi saurin katsewa, "
Aikuwa kamar yasan ta kunna a tym d'in yasake trying numb d'in sai gashi yashiga,"
Kallon phn d'in tatsaya yi har yakatse bata d'aga ba sanda, wani call d'in yasake shigowa ne ta d'aga,
Ajiyar zuciya yasauke wanda har cikin waya sanda tajii, "
Cikin worried voice yace, sweety I miss u,"
Batasan lokacin da bakinta ya furta I miss u mor,,,,, saurin Rufe bakinta tayi bata k'arasa ba."
Dad'ii yaji jin shima tayi missing d'insa. "
Sweety zanzo yau da daddare,"
Rufe baki tayi tace no karkazo, "
Meyasa?" yatambaya, "
Bazasu bari kaganni ba."
Nidai zanzo kisan yanda zakiyi yana fad'in haka ya kashe wayar baijira cewarta ba. "
K'arfe shida su amira suka dawo itada hameeda da kuma hafsat."
Suna zuwa dukansu suka zube jikin *hanna*  ihuu tasa tana turesu ni da'allah menene hakan kutashi, "
Hameeda ce ta d'ago tace beb kinga lefenki?"
Wallhy ko atarihi banta6a ji ko ganin wanda yasamu lefe kamarkiba, amirace ta nisa tace beb akwatunan talatin kamar amafarki, "
Beb duk kayan ciki kyawunsu bayi fad'uwa, beb ko rabin akwatin ba'@bude ba kowa yagaji,"
Hafsat ce tace kud'in kan akwatii kinsan nawane? "
Rufe mata baki tayi tace banson jii,"
Ganin zasu dameta da surutu ga lokacin magrib yayi yasata tashi tabarsu kamar wanda sukayi gamoo, "
Sallah tayi tazauna akan pray mat tana jiran ayi sallan isha azao akwa6a mata abun ajikinta,"
Wayanta ce tafara ringing dan tunda ta kunna bata kashe ba, tana dubawa taga MG ne. "
Tana d'auka yace mata yana waje,"
Futa tayi ta na sand'a har tafice agarden taganshi yana zaune kamar wanda yadad'e da zuwa, "
Kallon ta yakeyi tun daga nesa, da badan zuciyoyinsu na manne da juna ba da yayi musu cewa ba ita bane."
Har takaraso bai saniba kamshinta ne yasanar dashi isowarsa, "
Sallama tayi ta gaidashi ya amsa, sannan yace sweety kinyi kyau sunkuyar da kai tayi tana wasa da yatsunta," sanda sukafii mintii goma bbu wanda yasake cewa komai, kallonta kawai yake yi, " sannan yatashi yace natafii fligt d'ina 7:30 zai tashi akano nakeso nayi sallar isha, bud'e baki tayi tace dama kawai kazo, murmushi yayi sannan yace ganinki aiba kawai bane,"
Ahaka taraashi har bakin gate dake bai Shigo da mota ba leqawa tayi taga gidan zagaye da sojoji, "
Bud'e baki tayi tana kallonsu,"
Muryarsace ta dawo da ita kina mamaki ne? "
Tun randa aka kawoki gidannan suke zagaye dake, yana fad'in haka yajuya,"
 itama juyawa tayi da gudu ta shige gida, "
Nan sojojin suka k'arkame kofa,"
Juyawa tayi tana mamaki wato shiyasa kai tsaye yasan yanda take. "
Tana shiga bata samu kowaba tashige tayi sallah sannan akazo aka fara."
Yau takasance gobe za'a fara event duk wani shirye shirye anankai har makeup artist anrigada an shirya su yanda komai zai tafii dai-dai washe gari ya tashi ranar laraba ranrda za'ayi kamu tun safe aka fara shirye shirye. "



To be countinued





Ur's
      Z33yyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

 *_If a friendship last longer than 7 year's, u are not just a frnd u r family, "  just like we are *MAIMUNAT* *_this whole Page is dedicated to u my frnd,"_*
*_Wsh u safe journey y'an kano zasuyi missing d'inki_*😉

*
Page 52

 K'arfe sha d'aya 11:00 Suna zaune afalo, Suna shirya yanda kamu zai kasance,"
Sallamar labba kawai sukajii, "
Juyawa sukayi cikin mamaki, alokacin angama zanawa *hanna*  lalle kenan yayi masifar kyau irinna larabawa dan sunema suka zana mata."
Angama mata itada hameeda ana yiwa amira saura hafsat, nan labba tashigo itama tayi kyau sosai, ga zanen lallen ta yayi kyau saidai kawai baikai na *hanna*  ba. "
Wasu irin sirararn zane masu kyau har kyalli sukeyi da wani irin kamshi zanen lallen *hanna* ,"
Labba ne ta zauna tana subhanallahi 😍😘 antyna kinga irin kyau da kikayi? "
Wallhy Idan ahanya naganki ganeki zaiyimin wahala."
Kai gaskiya ya yareema yayi za6e, kin ganki kuwa? "
Har wani sheki kikeyi kamar wata taurqruwa,"
Harara *hanna*
Ta galla mata ta canja tapic na zancen da cewa yaushe kika iso? "
Tun d'azu tareda ya yareema muke ma kinga namanta,"
Zakuje kuyi pics d'in da za'ayi amafani dasu, kinsan fa bbu pics d'inku tare kuma duk abunda za'a buga sai an buqata shiyasa har yanzu bbu abunda akayi, "
Harara *hanna* ta mata tace nidai bbu wani pics d'inda zan d'auka, danna gane cewa, wayo zakiyimin ayi pre wedding pics kuma ai na fad'a miki bazanyiba."
Abuga abunbuwan haka kawai da sunaye basai ansa pics ba. "
Lallashinta sukayi tayi dakyar ta yarda dayin pics d'in.
Amma saidai su Shigo cikin gidan ayi bbu musu labba tasanar masa dan itama aganinta hakan yafii dacewa da kuma mutumcii."
Akwatii guda labba tashigo da shi na kayanda za'ayi pics d'inda su sannan mai makeup rines makeover kunsan yanda sukayi fice wajen kyafa amare, tafara yi mata light makeup ba za'ayi makeup d'in tayi heavy sosai ba dalilin zuwa jimawa za'ayi na kamu. "
Alokacin kuma MG na wajan frnd d'insa da suka iso dan kamun,"
Wasu frnd d'insa ma basu iso ba dan yawancii na k'asar ne kawai. "
Aranar anty samha da Abubakar suka iso,"
Gidan baba yasauketa shi kuma yawuce cikin sauran frnd d'insu. "
  Bayan angama makeup ne aka yiwa MG waya ya iso,
Alokacin aka shirya *hanna*  cikin atamfar holland mai ratsin green d milk tayi matukar kyau."
Masu d'auka pics sun dade da hallara,"
Su dript media, Ahmed zol, amana photography, Atunbi photography,  genius cenimatic style, buckles photography,  kai dayawan sudai dan bazasu irguba. "
Tun daga nesa yake kallonta dan wani irin masifar kyau tayi, itama anata wajen hakane wani kyau yamata sosai,"
Askin kansa ma kawai abun kallo ne"
Itada labba bane dama takara ta ganin yanda suke kallon juna yasa labba tana zuwa ta basu waje, "
Sunkuyarda kanta tayi tana wasa ta yatsunta ta gaidashi,"
Baibar kallonta ba yanacii gaba da kallonta ya amsa. "
Gashiya tayi da tsayuwa baice mata ta zauna ba, ta dago kanta tana d'agowa suka sake had'a ido," Alokacin idanuwansu yasarkafe acikin najuna brown d'in captain yasa, ya murza brown d'in hula da bak'in takalmi akafarsa."
Nan kuwa photographer's abunne ma yasamu aka fara d'aukan pics kala-kala, "
Alamu yamata da hannu tazo ta zauna bbu musu ta zauna kusa dashi, ya sunkuyo dai-dai kunnuwanta yana fad'in sweety kinyi kyau u luk like an angel,"
Dad'ii ne yakamata alokacin dariya ya subuce mata tasa d'ayan hannunta tarufe bakinta. "
Hakan da sukayi bakaramun kyau yayi ba,"
Shiyasa kawai sukacii gaba da d'aukan photo ahaka,"
D'agowa yayi da niyyar yace su d'auka nan yaga sun ma d'auka sukam. "

Kiran wayar labba yayi yace ke kizo kitafimun da mata da canja kaya kuma saura karki tafi da ita ahankali. "
Tana zuwa takama hannunta suka Shigo nan ma wata Exclusive tasa bak'in atampa da fari d'inkin riga da zanii,"
Aka d'aura mata kwalin tayi masifar kyau, har tafii d'azu had'ewa, "
Ganin yanda rigar ta matseta yasa tace bazata fita bbu gyale ba,"
Haka dole sanda aka d'auko wani farin gyale mai kyau ta yafa Ahaka suka fita shikuma yasa bak'in captan da bak'in hula, nan ma akayi pics suka dawo yayi kyau sosai, "
Sai na ukunne ne tasa super wax, jaa mai ratsin farii nan ma tayi kyau sosai shikuma yasa farin shadda sol."
Na had'u kuma arabian gown ne yellow tayafa farin veil, shikuma yasa yellow d'in polo da farin jeans,"
Gaskiya pics d'in ba k'aramin kyau sukayi ba, "
Sai suka fito kaman larabawan usull."
D'ayan shiganne kuma tace ita atafar bataga wanda ya'iisa yasata tasa trouser na jeans da polo tayi pics ba, "
Sanda abun yakai ga kiran ummii ta rarrasheta kafin ta yarda,"
Bakin jeans ne da pink d'in polo kowannen su yasa sai tayafa bak'in veil."
Agaban nata anrubuta he's mine." agaban nasa kuma she's mine, " abayan nasa *YAREEMA* anata *HANNA*
Duk kunya tabi tacikata dan jeans d'in bakaramin matseta yayiba," hips d'inta duk awaje, gara rigar ita tad'an sake
Gashi pics d'in kayan yafii yawa, sanda aka gama sannan ta d'auki after d'inta tasa tashiga, "
Ita atunaninta angama kawai tak'ara kallon wani kayan shima still riga da wandow,"
Golden ne rigan polo fur tak'i canja veil da wandow shima hakan yayi."
Abayan rigarsa prince anata kuma princess, "
Anrubata agaban nata Bride to be."
Shi kuma nasa groom to be. "
Sosai polo d'in tamusu kyau,"
Styles kala-kala sukayi ak'alla sanda suka canja kaya 15 set. "
Gajiya tayi tak'i,"
Dakyar aka lallasheta ta yarda tasa na soldier's na k'arshe, "
Subhanallah😍 kuso kuga kayan soldier's yanda ya amshi *hanna*  balleshi gogan, ana gamawa da gudu ta shige ciki," duk styles d'in da akayi bbu wani wanda yakaucewa sharia danko wajan d'aya bbu yanda jikinsa yata6a nata. "
Dariya kawai yayi dan yasan agajiye take. "
Tana shiga ta zube labba tatashi tafice dan tana bukatan pics d'in,"
Sai can ta dawo tazo tana nuna musu pics d'in awaya kowa sai kallo yake yi with odarable dan sunyi kyauwunda fad'an hakanma bata lokacii ne, " Cikin hour's pics d'in suka zaga duniya gabaki d'aya."
K'arfe biyu bayan *hanna* tayi sallah Suna zaune kawai sai ta window suka kallo anata squke souvaniers manya manyan jakkuna da su memo kai Idan natsaya fad'a ku kanku masu karatu zakuce nacika surutu, k'arshe dai hadda atamhopin hllond akowani jakka,"
K'arfe uku dai-dai aka fara shirin fara makeup, "
Amma *hanna* tak'ii fur tace sai tayi sallah hakan kuwa akayi,
Alokacin kawayenta sunfara shiri wasunsu ma, sun gama shiri, ana kiran sallah *hanna* tayi sallah sannan luccy makeover suka fara shiryata,"
Cikin 1 hour suka gama komai subhanallah kada kaso kuga *hanna* awannan lokaciin, "
Sannan tasa  dark pink na gown da net har k'asa."
Duk yanda ake fad'in kyau to *hanna* tayishi,"
Sai kuma k'awayenta suka sa maroon na material,"
Alokacin motocii suka fara sutsawa Cikin wajen, "
Anje can gida har an ebii mutanen can duka amarya da ango kawai ake jira,"
Sai motocii ne tun daga Cikin gidan har titin anguwar duka. "
Duk irin k'awayenta dasuka taru dan wasu kanma bata sansu ba amma kowacce kawa mota d'aya tashiga daga ita sai driver."
 *Hanna* ce tafito amira da hameeda sunsata atsakiya har gaban wata mota wanda tafii kowanne kyau suka wuce sannan suka bud'e shiga tayi kowa yakama gabansa, "
Kamshin turarensa ne yasanar mata dayana Cikin motar," bata juya ta ta kalleshiba har motar tafara tafiya, "
Wasa da yatsunta kawai takeyi,"
Shima baice komaiba kawai kallonta yake yi, "
Sanda suka isa sannan aka bud'e kofa azaranda hotel ne tun daga waje, wajen yake k'ayata, har wani kalli kalli tako ina yakeyi."
Koda da suka shiga komai na wajen ya burgeta, "
Bud'e masa kofa akayi yafito ya zagaya ya bud'e mata," sanda tafito kafin ta kalleshi farin shadda ne manyan kaya ajikin sa. "
Anyi aikin surfanii da pink d'in zare,"
Zai hula xanna k'arshen tsada zanna pink da farii, "
Ahaka suka k'arasa shiga, komai ya k'ayata haka akayi event aka gama,"
Komai yayi kyau Dangin MG sun yaba da hankalin *hanna* sosai, "
Da kuma kyawuta da karamcii irinna danginta."
Tunda suka d'auki hanyan komawa nanma bbu wanda yace k'ala,
Sai da tazo fita ne tatsincii muryarsa yana cewa "  Yau zan wuce kano sai ranar d'aurin aure kafin,"
Narai Narai tayi da idanuwanta tace kabari sai gobe kaga yau ka wahala, "
Murmushi ne ya kufce masa dan yaji dad'in yanda ta nuna kulawa agareshi yace" nabari in sha Allalh gobe da safe zan wuce, "
Murmushi itama tamayar masa tace tom Allalh ya kiyaye tana fad'in haka ta juya tafice."

To be countinued

Ur's

     _Z33yyb3rw3r_

[10/4, 7:18 PM] ‪+234 816 114 6563‬: *BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

   *_Alhamdulillah welcome to the world of islam_*_*(Abdurrahaman)Allah yaraya mana kai cikin addinin islama."*_
_*Welcome to our*_*world once again, "*_
*_Antyna Allah yak'ara karfin jiki."_*



Page 53


*
   Da gudu tashige gida,"
Girgiza kai MG kawai yayi yana mamakin yanda gudu bayi mata wahala, "
Sanda yaga shigrwarta sannan yajuya suka wuce tana shiga tazube akan gado dan ba k'aramin gajiya tayiba ga takalmin kafanta asalin hill ne."
Gabaki d'aya da takalminta ta zube, sanda hafsat tashigo kafin tacire mata. "
Zqma tayi kusa da ita,"
Ita kuma *hanna* tayi lying a bed ta lumshe idanuwanta,"
Hafsat ce tata 6ata tace, sis, bata d'ago ba kuma bata bud'e idanuwanta ba tace uhumm, "  tak'ara ce kekam sis kinyi sa'a wallhy duk wani abunda ake buk'ata awajen namiji, mijinki nadashi,"
Umm kawai tace dan batasan amsar da zata bata ba. "
Hafsat ce tak'ara cewa," 
Ni ma kitayani addu'a Allah yabani miji mai kyau Koda kuwa kwatan kwacin na yareema ne. "
Sai alokacin *hanna* ta bud'e idanuwanta ta tashi ta zauna sannan ta kamo duka hannuwanta biyu tace"
 Adda Hafsat ina labarinn mas'udd?" da kike neman wani kuma, "
Hafsat ne tace hmmm kibar maganan mas'udd kedai kawai kitayani addu'a,"
Nisawa *hanna* tayi sannan tace tom amma d'azu aina ganki da captain bilal awajen kamu duk da cewa bansan mai kuke cewa ba amma abun yamin kaman akwai wani abuu. "
 Nisawa Hafsat tayi sannan tace eyyerr nima naso hakan amma bahakan bane."
Wai yau bamu futo da wurii bane shine yak'ar6i phn numb d'ina akan Idan munshirya sai mu fad'a musu. "   
Umm *hanna* tace kawai dan bawai ta yadda dalilin hakanne yasa yak'ar6a ba,
Akwai wani dalilinsa daban,"
Jin ana kiran sallah yasa su tashi, toilet *hanna* taje ta d'auro alwala sannan tagabatar da sallan magrib sannan ta zauna akan sallayan sanda tajira akayi isha'ii sannan ta gabatar da isha'ii da shaf'ii da wutiirii, sannan tayi haramar kwanciya, phn d'inta ne tafara ringing dai-dai lokacin "   ko bata duba ba tasan waye zaikirata a dai-dai wannan lokacin,"
Nad'e pray mat d'in tayi sannan ta nufii wayan da niyyar d'auka, "
Kafin ta isah ta katse,"
K'ara kira akayi tana isa tad'auki wayan amma ga mamakinta ba numb d'in MG bane kamar yanda tayi zato,"
sanda ta isa bed ta zauna sannan tayi picking, "
Sallama tayi amma shiru tak'arayin sallama ba'a amsa ba, shiru akayi na tsowon 4 minute ita bata kashe ba kuma ba'ayi magana ba tun daga sallamarta kuma bata sake cewa komai ba sanda yacika 5 minute tayi niyyar ajiyewa tajii ance plz karki ajiye dannasan kina shirin yin hakan. "
Runtse idanuwanta tayi jin yadda muryan ta daketa,"
Ko mafarki bazata manta wannan muryan ba. "
Gabanta ne yahau fad'uwa da k'arfii kamar wanda k'irjinta zai fashe,"
Shiru tayi takasa, "
Tacikin wayan aka k'ara cewa nasan kina jina k'inki amsani ne."
Cikin rawar murya *hanna* tace mai yasa kakira? "
Ta Cikin wayar akace sabilida in jaddad miki cewa haryanzu inasonki?"
Cikin murya mai kamada t kuka tace najeeb kasan kuwa mai kake fad'a? "
Cikin wannan week d'inne fa aurena,"
Cikin rashin damuwa da abun da yake cewa da d'an tsawa-tsawa yace nasanii *hanna* nasanii basai kinfad'a mun zaki aurii d most richest hansome young man ba, "
Wasu siraran hawayenen suka fara bin fuskarta tasan tabbas mutane dayawa zasuyii tunanin cewa dan kud'ii ko kyau ko kuma mulki ko sarauta na MG zata aure shi, ita a  yanda takejii ko sonsa bbu azuciyarta har yanzu."
Amma hakanma bata fita awajen al'umma ba, "
Hmmm *hanna*  har indai zaki ce sai kinyiwa mutane dai-dai to har abada bazaki fita ba."
Kukane ya kufce mata tayi saurin rufe bakinta, "
Cigaba yayi da cewa,"
Tabbas nasan yanzu *hanna*  bakya sona kinsamu wanda yafini, "
Nasan namiki laipy amma *hanna*  nabaki hakurii a lokacin da nake neman afuwanki,"
Yakamata kiyafemin amma kika k'i har wata kaddarar tazo ta ratsa ta tsakaninu, "
 *Hanna*  maiyasa? maiyasa kika ki yarda da tuba ta a lokacin daya kamata?"
Maiyasa zaki maida rayuwarmu hell? "
Kinsan mai kike shirinyi kuwa Kinsan cewa daga yanzu Idan kikayi aure munrabu kenan har abada."
  Wai meyasa Kafin ki amince bakiyi tunanin yanda rayuwarmu zata kasance ba." *Hanna* itadai kuka kawai takeyi dan batada bakin cewa komai, "
Ko ayanzu tasan tanason najeeb amma kuma ba kaman sonda take masa da ba."
Sannan kuma ita batason MG amma tana kallon girmansa da kuma kumarsa had'e da darajarsa, "
Ko babu komai mutumin dayake sonka ba abun wulakantawa bane."
Zamanda tayi ta MG duk da shi bamai fidda abun cikinsa bane amma ta tabbatar da irin sanda yake mata. "
Wanda Idan za'a kasashi goma zaiyi wuya najeeb ya d'auki uku."
Irin abubuwan da take masa Koda najeeb da bai kaishi komai ba tasan ba d'auka zaiyi ba. "
Akullum yakan k'askantarda da kansa Idan yana tare da ita duk wani mulkii da sarauta yakan saukesu."
Muryar najeeb ne takatse ta daga tunanin data lula. "
Yace *hanna* nasan kinyii nisa,"
Allah yabada zaman lpy yana fad'in haka ya katse wayar, "
Yana katsewa *hanna* tazauna tana kuka kamar ranta zaifita."
  Ahaka har k'arfe tara na dare yayi tana kuka fuskanta duk ya kumbura. "
Sunyi lu6u-lu6u,"
Muryarta har ya dashe. "
Har dushu dushu take ganii ga wani irin ciwon kai daya daya rufeta."
Jitakeyi gaba ki d'aya ta tsani auran."


Ana haka anty maman amal tashigo tazo kawo mata aika ta ganta cikin wannan halin."
Zama tayi tana tambayanta maiyasameta?"
 Shiru tayi batace komai ba, "
Sanda ta rarrasheta tukunna cikin kuka tace,"
Anty wallhy nafasa auran ni bana sonsa. "
Duk da ran anty ya6aci tace, mai kuma yayi zafii *hanna* saura kwana uku ne fa d'aurin aurenki."
Eh anty dan girman Allah kitaimakamin wallhy nafasa auren,"
Cikin rarrashi anty tace, *hanna* kinason maida mahaifan mu k'ananun mutane kenan."
 Tayaya kike tunanin cewa zasu sami iyayensa suce anfasa aure? "
Kinsan cewa mutumcinsu ne zai zube."
Girgiza kai *hanna* tafarayi tace wallhy anty jinakeyi idannayi aurennan kamar wanda zan mutu."
 Anty dan Allah kitaimakeni wallhy zuciyana k'unci takemun."
  Duk wani rarrashin da anty tasan zata mata tayi amma *hanna* firr tak'ii."
Har ranta yafara 6acii, "
Cikin hasala anty tace tom Idan kikace bakya sonsa wakike tunanin zaki aura?"
Share hawayenta tayi tace,"
 Anty najeeb, najeeb zan aura, "
Wasu tagwayen marii Anty ta d'auketa dasu ta kowani bangare lokacii d'aya yatsunta yafuto atafin fuskanta."
Kuka *hanna* tak'ara fashewa dashi Jin zafinn marin, "
Cikin masifa Anty tace dan ubanki to najeeb d'in da kika nacewa an dad'e dayi masa mata."
Tun kafin kisan zaki amince da auren MG iyayensa suka za6a masa mata. "
Tun lokacin da kuka samu sa6ani basu bari kun dai-dai ta ba suka nema masa mata."
Kuma yamusu biyayya ya amince amma ke dayake banza ce marar tarbiya kika nace masa. "
Naki za6in iyayen kuma kika nuna ke basu isa dakeba."
 *Hanna* gaki ga duniya kije ki har indai maganar iyayenki ne bazaki bi ba, "
To wallhy kin had'u da Ganin jarabawa a rayuwarki."
Tana fad'in haka tatashi tafice daga d'akin ko aikan data kawo mata bata samu ta bata ba. "
Tana fita ta wuce gida dama tana driven da kanta."
Gida kawai tawuce. "
Tana tafiya tana tunanin halii irinna *hanna* shegen taurin kai kamar y'ar mayu."
 Ita kuwa *hanna* kulle d'akin ta tayi tacii kukanta, "
Wato najeeb yakirata ne dan ya ruguzamata d'an farin cikin data samu tashiga kwana 2, shiyanacan aure ake shirin yi masa amma tunani yakeyi ta yaudareshii."
Kuka ta k'ara fashewa dashi ga wani irin rad'ad'ii da zogii da fuskanta yake mata tashi d'aya zazza6i ya rufeta. "
Gashi ta kulle k'ofan da key tanajii su amira Suna ta bugawa amma jikinta yamata nauyi bazata iya tashi ba."
MG yayita kiran wayar ta amma bata iya d'agawa ba."
Sai yabar abun a gajiya kawai yace yanaga tayi bacci."
Sai k'arfe shida *hanna* tatashi gabaki d'aya fuskanta ta kumbura dan kusan kwana tayi tana kuka sai a lokacin tayi sallah. "
Bayan ta idar tatashi ta bud'e kofa."
Bata dad'e da bud'ewa ba su amira suka Shigo ganinta Ahaka yasa sukayi saurin k'arasawa Suna tambayanta maiyafaru? "
Kawai ce musu tayi ta kwana da zazza6i ne,"
Ahaka sukayi ta tausaya mata harsuna mata fad'an rashin kiransu da batayi ba kuma sunzo k'ofa a arufe. "
  Ahaka sukayi ta janta d tad'ii dan bbu yanda basuyi tasha magani ba tak'ii." K'arfe had'u suka shirya zuwa family and friend MG bazai samu hallara ba dashi har ya wuce."
Ahaka tayi kyau sosai amma kowa yaganta saiya fahimcii cewa tana tattare da damuwa." shima a *zaranda hotel* akayi."
Abu yayi kyau sosai bayan angama antafii,
Labba taturawa MG pics d'in yana kallo ya gano cewa Akwai abun da yake damunta ko shiyasa yayita kiran wayarta ba'a d'aukaba,"
Amma yayanke shawarar kiranta yajii komenen yake damunta. "
Ba abunda yadamu *hanna* kamar rashin ganin Anty dabatayi ba awajen event d'in tabbas tasan ta 6ata mata rai."
Hakanne yak'ara mata wata damuwar. "
Bayan sun dawo gida ko hutawa batayi ba wayanta yafara ringing tana dubawq taga MG bata ja lokacii ba ta d'auka dan tasan tun jiya yake nemanta."




To be countinued



Ur's
      *Z33yyb3rw3r*
[10/4, 7:23 PM] ‪+234 816 114 6563‬: *BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

 

Page 54

    Srry, Srry, Srry, 😭😭😭😭😭😭bason raina bane kuka jini shiru. "
Al'amura sunfii k'arfii nane."


*
  Fita tayi daga cikin mutane ta nufii d'aki, sannnan tayi sallama, "
Ajiyar zuciya ta sauke amma dukda haka ya fahimcii damuwa cikin muryarta."
Amsa sallamar yayi baijira gaisuwarta ba ya fara tambayarta meyake damunta?
 Wasu siraran hawaye be sukaa bi kan fuskarta sa bayan hannun ta tayi ta goge hawayen sannnan tace bbu komai. "
Nisawa yayi sannnan yace plz kobaza ki fad'amun ba, nasan wata damuwar fad'anta baida amfani amma kuma kicire damuwa aranki, kokad'an banason ganinki cikin damuwa,"
Hakan ba k'aramun ta6amun zuciya yakeyi ba. "
K'irkiro murmushi tayi kamar wanda yake kallonta, tace masa bbu komai ba kawai stress ne yamin yawa."
Ya gamsu sa maganarta dan ya tabbata hakan ne. "
Ahakan tad'an sake suka ta6a hira."
Naan yake shaida mata cewa gobe bazai samu yakirata ba, dan gobe duk Wasu frnd d'insa na k'asar waje zasu iso kuma dole zaizama busy. "
Ahaka sukayi sallama,
Kwanciya tayi tafii 30minute.ita kan ta batasan mai take tunani ba amma tasamu kan ta sa jin damuwarta ta ragu." takai kusan awa d'aya ahakaa, "
Kiran sallar ishah ne yatasheta daga kwanciyar da takeyi." tatashi ta d'auro alawala tayi magrib kafin tayi ishah tazauna tana ta azkhar sa addu'oiin naiman za6in alkhairii. "
Ahaka ta kwana sai kusan 3am.ta kwanta,"
Sanda takusan makara sallar subh,"
Dan sai shida tayi sallah. "
Koda ta idhar nan ma azkhar tayi tayi har k'arfe bakwai sannnan tayi Kwanciyata."
Ko Fita batayi ba sai bacci kawai takeyi."
Sai 10am. Tatashi tayi brush sannnan tafita dan karyawa, su hameeda kuwa basa manan dan abubuwa hidin dimunsu har yafii na amaryar, "
Barinma yanzu sun had'u sa labba, abubuwan dai sai ahankali dan duk wani hidima dayakamata amaryar tayi su sukeyi sai dai sukawo mata."
Fita tayi tatarda ankawo mata abin cinta, dan dama nata daban ake tanadar mata, "
Zama tayi tacii abincinta sosai wanda ta dad'e bqtacii abuncii hakaba dan yanzu ta d'aura niyyar cire duk wata damuwar dake cikin ranta."

Bayan tagama cin abincinne ta d'auki wayarta haka kawai tajii sha'awan kunna *data* dan takai satii bata kunna ba."insta tafara leqawa ta Ko ina tayi pics d'insu take ganii barinma kamarsu weddingguet, arewa hausa fulanii, xclusive wedding, nigerian wedding, couple goals. "
Kai tako ina pics d'insu ne abin har mamaki yake bata ga irin wani kyau dasukayi a pics d'in kamar me?"
Duk da tasan bata daga cikin irin masu masifar kyau d'innan amma kuma tanada nata dai-dai gwargwado, "
Kuma a pics d'in zakasha mamakin kyawun da tayi."
Kodan ayanzu hakama tayi kyau sosai har wani sheqii takeyi."
   Ahaka ta leqa can ta leqa nan, "
Massages kuwa kamar zasu cinyeta."
Gajiya tayi kawai tasauka."
Sai kusan azahar su amira suka shigo agajiye liqis. "
Sanda sukayi sallah sukacii abincii, sannnan *hanna* takalli amira tace babe dan Allah ga numb d'in yaya jalal zaki k'ar6omin gyalenda zansa yau, yana wajansa."
  Wani dogon tsaki hameeda taja sannnan tace to banda abin yaya jalal yanzu wani mutane ne acikin gudannan dazaice bazai zoba *Hanna* ba tace komai ba, tajuya ta kalli amira tace plzz babe kije ki k'ar6omin umma ne ta aikoshi shikuma yace bazai shigo ba. Dan baima shigo sokoto road ba yana kano road yana jira, "
Tashi amira tayi tace toh barina kar6o yanzu."
Tana futa *hanna* takirashi tace yaya jalal ga amira nan zatazo ta k'arba to kawai yace ta kashe wayan. "
  Tana futa tad'anyi tracking zuwa kano road can tahango motarsa atsaye, yana kallonta yafito daga motar yak'araso zuwa wajan ta."
Tun daga nesa yake kallonta yanajii wani zuciyarsa ba bugawa da saurii da saurii tunda yake bai ta6a jin wani abuu haka akan wata y'a mace ba sai akan *hanna* wanda ayanzu ya kawarda hakan, sai gashi kuma yanajiin hakan akan k'awarta. "
Wani irin kallo yake mata Tun daga nesa wanda ita kanta takasa jurewa kallonda yake mata." k'ananun kayane ajikin sa sun bala'in yimasa kyau. "dan ita kanta yamata kwarjini."
Ta sunkuyarda kanta har ta isa wajansa. "
Tana zuwa tad'an rusuna ta gaidashi ya amsa yana mai binta da kallo."
Wata irin murya yayi amfanii wajen cewa kinzo k'ar6awa k'awarki aika ko. "
Gabanta ne yafara fad'i dan Wani yanayi ta tsincii kanta dashi ga Wani irin kunyarsa data lullu6eta,"
D'aga masa kai kawai tayi. "
Ta mika hannu da niyar kar6ar laidain hannunsa yayi saurin zanjeyawa da'agowa tayi ta marairaice idanu tace ana jirana na nefa,
Shima irin muryarta yayi yace to muje in rakaki dan baza ki d'auki kaya ba."
Shagwabe fuska tayi tace wannan har Wani kaya ne dazakace wai kaya. "
Inuwa yananema yazauna sannna ya nuna mata itama tazauna bbu musu tazauna dan tafarajin dad'in hirar tasu,"
Haka ta zauna sukayita hira gasu dukanku masusan barkwancii, nan da nan suka saba. " basusan lokacii yayi nisaba sai kiran hameeda taganii."
Tana dubawa taga har 3 tasan komadai menene yanzu anfara shirin tafiya walima tashi tayi da saurii ya kalleta ina zakije muna tad'i? " yaya ka kalli lokacin tafiya yayi ni bansaniba, dan tsaki yaja yace kibari zan kaiki, marairaice fuska tayi kamar zatayi kuka tace" *hanna*  bazatajii dad'ii ba, "Tashi yayi
Sanda yarakata har bakin gate kafin yajuya."
Tana shiga tasamu kusan duka sungama shiri saura amarya da ake mata makeup kamar munafuka tashigo tashige toilet tafara wanka kafin tashigo tafara shiri."
Zuwa hud'u sungama shiri sai wajan 4:20.suka isa *awala hotel*  malama juwairiyya ne tayi wa'azii, zuwa 6pm.an tashi koda, suka koma gida abinda yadamu *hanna* har yanzu bataga anty maman amal awajen walimar ba kuma ta tabbata fushi takeyi dalilin dayasata kuka awajen walimar kenan, mutane dayawa sukayi zaton cewa wa'azine yaratsa ta."
Tadawo takira wayarta kuma ba'ad'aga ba. " ba'awuce ko ina dasuba sai gidan babanta dan gobe yakama d'aurin aure kenan."
Ahaka ta kwana bbu kuzari gawani irin fad'uwar gaba dan tasan daga gobe zata bar gida kuma saidai tazao yawo ko hutu kukakam awannan daren tayishi bbu iyaka. "
Washe gari da safe yakama asabar ranar d'aurin aure kenan."






  _Kuyi hakuri ku kar6i uzurina wallhy, nima kaina banso hakanba_



To be continued





Ur's
    *z33yyb3rw3r*

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_


_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

    Yaban gwani yazama dole gaskiya action kinyi k'okarii a littafinki na *saiful maleek*  Allah yak'ara basira da zaqin hannu, "
  Muna biyeda ke abuk dinki nagaba."
  Kinyi k'ok'arii wajan kammala buk dinki dawurii Allah yqtqimaka. "
  Ina tayakii murnar kammalawa."


Page 55

*
Dasafe haka tatashi duk jikinta bbu k'arfii dan kukan datasha jiya da daddadre, "
    Tun sassafe bak'i suka k'ara cika gidan tamm bbu masaka tsinke danma Allah yataimaka gidan yanada d'an girmansa."
  Auren za'a d'aura shine a masallacin a babban masallacin fahda dake bauchin yakubu."
   Can kano kuwa su MG sai shirin tafowa d'aurin aure akeyi, "
   MG kuwa yana shashinsa tareda abokanan sa wanda sukazo daga k'asashe daban daban."
    Shahid mahmud abbas, dakuma hamood bn abid ne kusa dashi suna zaune, "  banda tsokanarsa bbu abunda sukeyi gabaki d'aya tare sukayi passing out,"
Idan baku manta ba ashekarar dasu MG sukayi passing out a rusia nafad'a muku su uku ne."
Kuma dukansu musulmai ne, so sun zo bikinne, dan sukam sunyi aure. "
   Yayinda Shahid yaransa biyu shi kuma hamood d'ansa d'aya,
Alokacinda sukayi aure bbu irin takurawa wanda basuyiwa MG ba Amma yak'ii,"
Shi yasa yanzu suka sashi agaba suna tsokana, "
Shiru yamusu kawai yana murmushi dan wani irin nishad'i da farinciki yake ciki."
   Ko bbu komai yasan ayau zai mallaki *hanna*   yauce ranarda yayi shekara goma ciff yana jira, "
To dan maiyasa bazaiyi farinciki ba."
   Murmushi kawai yakeyi yana shafa gashin kansa, "
 Baice musu komai kawai da ido yake binsu."
     Hamood ne yatashi ya kalli MG yace"  soldier nifa tun jiya bansa matata a ido naba dan haka katashi kaje ka kainii wajanta na ganta."
   Murmushin rainin hankali MG yayi sannan yace ai Idan kaga nafita anan to katabbata cewa nafita ne da nufiin tafiya aje a d'aureni da sweery ne,"
   Idan bahaka ba kam ina nan yanzu ma barina tashii plzz  katashi ku shirya karkumuyi latti dan, "
 Sake baki sukeyi suna kallonsa tunda suke basu ta6a tunanin cewa MG zaiyiwa wani abu zumud'i hakaba,"
  Ganin haka yasa kowa fara shiri kafin k'arfe tara 9:00.am duka abokanan ango sungama shiri,".
MG kuwa farar shadda yasa karrr babbar riga gara." tasha bak'in aikii, "
Da bak'in hula gashinsa yakwanta yayi luff luff,"
  Da bak'in takalmii sau ciki sai shek'ii yakeyi. "
   Sai link dayasa a hannun rigarsa ta ciki, links d'in black diamon ne,"
  Kai alikacin kaga MG sai numfashinka yad'auke bak'aramun kyau yayiba Idan ana fad'in kyau to ina nufin kyau Kai ni aganina kalmar kyau tayi ka d'an ta fasaltashi. "
Koda yafito abokanansa tsayawa sukayi suna kallonsa,"
Dan sunsan yanada kyau Amma kuma nayau dabanne dakuma yahad'u da fara'a da kuma yanayin farinciki dayake ciki, "
 Sai kyawunsa yak'ara bayyana,"
  Futa yayi ya nufii shashin Unmii yayinda abokanan sa suka take masa baya har zuwa sashin Unmii Koda yashiga yasameta itama tayi shiga ta alfarma tayi wani masifar kyau. "
Sai annashuwa yakeyi tako ina hakwaranta awaje yake ga y'an uwanta sunsata agaba sai hira mai dad'ii suke yi,"
  Alokacin MG yayi sallama yashigo tundaga nesa Unmii ke kollon d'an nata wani irin kyau dayamata da wani k'ayataccen murmushi afuskarsa, "
Kana kallonsa kasan yana cikin farinciki marar misaltuwa."
    Koda yak'araso zuwa yayi ya zube guiwowinsa agabanta, "
   Saurin sa hannuwanta tayi ta rige k'qfafunsa Tana magana tanacewa mai son katashi kada ka 6ata wannna kwalliyar dan banso ko kwayar zarra ta kura ta sauka ajikinka harsai wanda akayi kwalliyar dominta taganii."
  Mai son ina matuk'ar farinciki yau in sha Allah burinka zai cika yau in sha Allah zan kalli ranarda nadad'e ina jiranta. "
Allah yamaka albarka yabaka zaman lpy arayuwar aurenka,"
  Allah yarabaka da duk wani sharrii da fitintunuu da zasu taso cikin aurenku. "
   Ahaka tayita masa addu'a masu matuk'ar mahimmancii har sanda yaji hawaye na k'ok'arin zubowa a idanuwansa,"
Ganin yanda idanuwansa suka cika da hawaye najin dad'iin addu'arda mahaifiyarsa take masa. "
   Girgiza masa Kai Unmii tayi tace a'a mai son ko ka manta yau ranar meyece?"
   Dakake shirin yin kuka."
    A'a karka fara katashi kaje ku tafii kar Kuyi latti. "
  Had'a hannuwanta biyu yayi ya sumbata sannan yace ba kuka zanyiba ummiina,"
   Ummiina kokin manta waye d'ankii. ne."
   Ummiina na d'ankii fa jarimii ne,"
  Kawai dai najii dad'iin addu'ooiinkii ne. "
  Inasonkii ummiina," Inasonkii fiyeda kowa aduniyar nan,"
Kinfii min kowa da komai mahimmancii. "
Allah yabanii ikon yimiki biyayya,"
  Sa hannu tayi alips d'inta tamasa alamun yayi shiru shhhh tashi katafii Allah yamaka albarka amsawa yayi da amin, "
   Mutanen d'akin duk sun zuba musu ido gabakii d'aya sai d'a da uwar suka burgeshi sai rayuwarsu tabasu sha'awa."
  Yatashi haka sanda ya sunbacii umminsa agoshi kafinnan ya gaida mutanen wajen yajuya zai fita, "
  Yak'ara juyowa yakalli amminsa yace Inasonkii ummiina,"
Murmushin ta mayar masa tace nima inasonka d'ana sosai Ahaka yafice yanufii shashin kilishi, "
  Koda ya isa yayi sallama ya jira akamasa isoo ya shiga, ta na kallonsa afili tanuna tana farinciki a zuciyarta kuwa ba haka bane." bak'in cikin Auren bare dazaiyiibe makill. "
   Koda intisar tajii muryarsa saita futo ganinsa haka da wani irin kyau dayayi ga annashuwa da farinciki afuskarsa,"
Ba k'aramin kishi bane ya turnuk'eta,"
Tasan wannnan farinciki da annashuwa duk dan zai aurii watane take idanuwanta suka cike da kwalla. "
Dkayr ta iya gaidashi ya amsa da fara'a sosai haryana tambayarta yatakwana hakan kuwa bak'aramun dad'ii yamata ba ko bbu komai yau tasamu dariya da kuma kulawarsa."
  Daganan yafice kilishi namasa addu'ooiin zaman lafiyanda ko zuciyarta bata kaiba. " Daganan wajan mai marataba yanufa yaje yasamu harya gama shiri su ake jira. "
   K'arfe goma dai-dai suka tashi damai martaba da iyalansa dakuma y'an uwa da abokanai zuwa wajan d'aurin aure."
Dake ajirgi ne basu dad'ee ba suka isa, "
Agidan mai martaba sarkin bauchi suka yada zango k'arfe shad'aya masallacii da wajan sun cikin bbu masaka tsinke."
   Jama'akam fad'ansu 6ata baki ne sojoji birjikk ta ko inaa, "
   Fararen fata sunfii kowa yawa awajen bikin,"
   Dan idan kaga taron wajen zakace taron k'asa da k'asa akeyi k'arfe shad'aya da rabii 11:30 dai-dai aranar asabar ranar rana mai dum6in tarihi aka d' aura auren *Abudullahi abdul'aziz lameed'o da hannatu muhammad dambam*   akan sadakii naira dubu hamsin ka call."
  A dai-dai wannnan lokacii gaban *hanna* yayi wata irin mummunan fad'uwa. "
   Jitakryi kamar tasa hannunta akayi ta kwala ihuu."
  Yayinda shikuma MG alokacin wani abuu daya tokare masa makoshi tsawon shekara goma sai alokacin ya fad'a. "




To be countinued



Ur's
     *z33yyb3rw3r*

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

Page 56

*
  Abinda yatokarewa MG kirjii samada shekara goma, "
  Sai alokacin da yajii and'aura aurensa da *hanna* kafin yajii abin ya fad'a masa sai wani irin sanyii yaringa jii zuciyarsa namasa,"
   Fara'a kawai yakeyi bakinsa kamar gonar auduga, "
   Sai gaisawa da y'an uwa da abokan arziki yakeyi tako ina,"
   Yayinda ita kuwa *hanna*  tun lokacin da taga 11:30 dai-dai yayi ga wani irin fad'uwar gaba dake damunta tasan cewa aikin gama yarigada yagama, "
Kawai ta tsincii kanta da hawaye dan ko k'arfin kukan batadashi dake ta dad'e tanayi."
   Kuma tanajii ana tad'ii ta window cewa k'arfe d'aya bayan anyii reception zasu kama hanya."
   Cikin ranta tanajin wani zafii da rad'ad'ii sai kace wanda suka gajii da ita zasu bada ita k'arfe d'aya. "
   Ahaka ta zauna bbu yanda Ammah batayi da ita tayi wanka ba Amma firr tak'ii yii babu irin lallashin da batayi mata ba Amma tak'ii,"
  Ganin lokacii yawuce yasa Amma taje tafad'awa mama, "
  Duk da mama itama najin zafinn rabuwar ta da d'iyarta tadaure ta shiga tafarayi mata fad'a."
    Sai alokacin *hanna* tasamu bakin yiin kuka tajuya takalli mama tace,"
 Hava mama kumin dasauk'i mana tafad'a tana wani matsanancin kuka,"
Hava mama tafiya fa zanyi na barku Amma bazaku barnii naji da d'aya ba? "
 Mama yazanyi nashiga uku tafad'a tanamai fashewa da kuka."
   Nan da nan idanuwan mama itama yaciko sosai, tausayin y'ar tata yayi bala'iin kamata," Tashi tayi da sauri tafice daga d'akin dan idan bahqka ba zuciyarta na iya tsinkewa tafashe da kuka."
  Mama bata wuce ko ina ba sai dak'in ta tana zuwa ta zube tana sauke ajiyar zuciya, "
  Ganin haka yasa umma matsowa kusa da ita tana tamvayar maiyafaru duk da tasan cewa yau Mama sai ahankali rabuwa da d'iya yanada matuk'ar ciwo."
   Matsowa tayi kusa da ita ta dafa ta. "
Sannan tace hava aisha yanzu idan ke baki dauree ba tayaya kike tunanin yarinyar zata daure?"
Nasan da ciwo Amma hakuri zakiyi bayau fa kika fara aurar da d'iya ba dan haka kiyi hakuri ko itama yarinyar zata samu ta kwantar da hankalinta."
  Girgiza  Kai Mama tayi Sannan tace kayyah yaya wallhy wannnan ba irin way'ancan bane kada ki manta, "
Auren hajja nayi tunani Akwai wata agabana sannan auren hindu shima ta barmin *hanna* yaya kike tunani zanjii yanzu idan aka d'aukemin ita?."
  Banida wani mai taimakamin kinsan kulawar y'ay'a maza ba kamar na y'ay'a mata ba."
 Goge kwallar data zubo mata tayi Sannan tace yaya kije ki rarrasheta dan tak'iyin wanka,"
Jikin umma ne yayi sanyi liqis Sannan ta tashi ta nufii d'akin Ammah bata reda tak'ara maganaba, "
  Azaune tasamu *hanna*  tana sheshekar kuka,"
   K'arasawa kusada ita tayi ta dafa ta, cikin muryar lallashi tace, "
   Hava *hanna*  mekikeyi hakan?"
 *Hanna*  kiyita kuka sai kace wanda aka miki auren dole? "
  Hava *hanna*  kada ki kasance marowaciya mana kada ki kasance wanda bata sowa mahaifinta rahamar ubangiji."
    Ke kanki shaida ne wannnan ingan taccen hadisi ne cewa duk mahaifinda ya aurar da y'ay'ansa samada biyu zuwa gidan mazajensu lpy,
 Suka kare mutumcinsu Allah namasa albishir da gidan aljanna. "
  Kukan *hanna*  ne yatsagaita Sannan umma tacigaba da cewa,"
   *Hanna*  kisowa mahaifinku wannnan rahma, "
  Kiyiwa mahaifinku biyayya dan samun wannnan rahama."
    Ahaka umma tayi ta conviceing nata ta tashi tashiga wanka, "
  Tana fitowa tayi umma ta bata mayuka kala kala ta shafa,"
  Sannan ta bata turaruka samada kala shabiyar ta shafa, "
Kuma duka masu sanyiin kamshi."
  Sanda tagama shafawa Sannan umma tace tazauna ayi mata makeup Amma firr tak'ii, "
Haka umma takyaleta bata matsa ba, dan tasan ko anyii zuwa jimawa idan taga anzo tafiya da ita zata 6ata da kuka."
   Haka tad'uko mata wata bak'ar exclusive mai ratsin farii dinkin riga da zani anyi plain na zanin. "
  Yazauna ajikinta d'an kwalin kuma tad'aurashi kawai batareda tayi wani style ba tazauna kawai tana tunani sai alokacin umma takawo mata tea da masa akan tacii,"
   Dkayr tad'an tsakula dan d'acin abincin takeji, "
  Tea d'inma dakyar ta kurba d'an kadan Sannan tace ta koshi."
    Su kuwa can suna *faria suite limited*   suna reception, "
K'arfe 12:30 zasu gama,"
      Dazaran sungama za'atafii da amarya, "
K'arfe 12:40 suka gama reception alokacin motocii suka nufii gidansu dan d'aukan amare,"
    Alokacin aka kira *hanna*  zuwa d'akin baba anan tasamu duk y'an uwanta aciki Nasiha kowa yake mata sosai daga wannnan yagama wannnan yake kar6a, "
Itakuwa Mama takasa cewa komai duk jkinta yayi sanyi sosai."
   Hawayene yake ambaliya afuskarta,"
Tanajin k'aran isowan motocii tayi saurin rarrrafawa gaban baba tana kuka tana cewa baba kamin rai natuba nabi Allah kayafemun baba karka bari su tafii danii. "
   Wallhy baba idan wani abuu namaka nadaina baba bazan sake ba."
   Baba bansan baka sona ba wallhy dakana sona bazaka bari su tafii danii ba,"
 Ganin baba ya sunkuyar da kansa yasa ta rarrafa wajen abba tariqo kafarsa tana kuka abba kumin rai natuba nabii Allah nabiku abba kutaimakenii. "
  Wani irin tausayin ta cikin matan kuwa d'ai-d'ai wayanda basu fara hawaye ba."
    Ganin abba bai kulata ba yasa ta rarrafa gaban anty maamn amal, "
  Tana kuka tana anty dan Allah kiyafemun, kiyi wa su abba magana."
    Anty maman amal ce ta rungumota tana cewa baki min komaiba kanwata, "
Wallhy ban kutace kiba,"
Ba kawai inaso ki fahimcii Abinda yakamata kiyi ne."
   Amma kiyi hakuri *hanna* gata ake maki ba wani abun ba. "
    Aure gatane agareki, aure shine martabarkii."
    Kiyi hakuri Ahaka matanda sukazo dauk'anta, sukayi sallama, "
Tana jinsu k'arfin kukan ta ya k'aru,"
Ahaka suka shigo aka gama duk wani abuu daza'ayii, "
   Aka rufa mata abaya aka nufe waje da ita."

To be countinued

Ur's
    *z33yyb3rw3r*

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

Page 57

* A dai-dai wannan lokacii *hanna* kuka takeyi kamar ranta zai fita, "
 Kuka takeyi kamar wanda akace har abada bazata zo gidanba."
  Kuka takeyi tamkar wanda akace mata mahaifiyarta ta rasu. "
   Fulani ce riqe da ita d'ayan gefen  kuma umma,"
   Sai baki umma ke bata, "
   Alokacin aka shigar da ita wata mota k'irar *marcedeze benz* E350,
   Yayinda duk sauran motocin corolla s ne wanda *hanna* kad'ai zata shigane ya banbanta,"
  Haka *hanna* tanajii tana ganii aka turata cikin mota aikuwa saleem na gefen ta shima idanuwansa taff hawaye caff ta cafke hannunsa bbu yadda ba'ayi tasakeshiba amma fir tak'i duk da mabiyi da mabiyi bbu shiri amma akwai soyayya a cikin zuciyya ganin Haka yasa amma tace yashiga gaba,"
Yana shiga sannan umma ta shiga d'ayan gefen fulanii ta shiga d'aya, sukasa *hanna* atsakiya suka d'auki hanya."
   Amota Sai lallashin ta umma keyi, Fulani tace rabu da ita tayi abunta ai girman kenan, "
Yanzu idan batayiba Sai ace tayi rashin kunya,"
   Tafiyar mintii 25minute ce tasadasu da airport."
Dan acikinsu akwai wanda zasu tafii Amota amma Sai sun raka amarya airport."
  Sabilida anason isan amrya ta isa da wuri akwai abubuwan da za'afara shiryawa kafin diner kuma anaso tahuta, "
Ga kuma Fulani tsufa yafara kamata bazata iya tafiya mota da nisa ba."
  Ahaka suka futa *hanna* da k'awayrta da kuma sauran y'an uwa najiki suka nufii jurgin, "
   Sukuma sauran suka nufii hanya,"
  Suna sauka motocii aka shurya na zuwa tar6ansu da iyalan gidan mai martaba Suna juransu, "
  Sosai aka musu tar6an karramawa gashi duk airport d'in da algaita kawai yacika ko ina,"
   Harda kilishi wajan taryan amarya, "
  Sai murna takeyi tana rungumeta kamar da gaske da kuma y'an uwan ummii, suma sunyi murnar ganinta,"
Kowa Sai hugging d'inta sukeyi. "
Alokacin *hanna*  harta bar kuka ajiyan zuciya kawai take sakewa."
 Ahaka aka d'ugunzuma zuwa fada, umma ce ta rad'a mata akan tasauka da k'afar dama hakan kuwa akayi."
   Sanda aka kaita duk wani shashi na gidan ta gaida Kowa sannan aka nufii shashin da MG ke ciki Yanzu tazauna na d'ayan gefen upstair ashi zasu zasu zauna."
Sun mace wajan kallon shashin wasu kanma sunyi zaton nanne wajan zqmanta. "
Duk wanda yashiga wajan saiya yabawa wanda ke zaune awajan gurin tsafta Dan komai farine har kyalli sukeyi."
Labba ne tabud'e d'akin da MG ke kwana tace *hanna* tashiga d'akin shiga tayi itada hafsat hameeda da amira, "
  Sauran kuma sauran d'akunan aka bud'e musu."
Wani irin kamshi shashi yakeyi, "
Barin d'akinda su *hanna*
  Kam ba'a magana," kamshin har wani fusgarsu yakeyi. "
  *Hanna* ta shiga tayi wanka tasa doguwar riga kawai ta kwanta akan gado tana tunanin gida."
  Kamshin pillow d'inne yasata lumshe ido daganan bacci yad'auketa."
   Sai kusan k'arfe hud'u wanda suke mota suka isoh."
 Shashin da *hanna* zata zauna sukaje suka ganii sunhanallah iyayen *hanna* sunyi k'o'ari wajan tsara mata d'aki. "
   Ahaka suka futa Kowa Sai san barka yakeyi,"
Gidan abba suka wuce daganan zasu wuce diner. "
  Hanna bata farka ba Sai k'arfe biyar,"
Tatashi ta watsa ruwa taqara komawa ta kwanta itaba bacci takeyi tunanin abubuwa kawai takeyi. "
  Misalin 6:00.pm aka fara shirin zuwa diner Dan 8:00.pm za'afara,"
   Kafin saven mai makeup sunzo, "
 Sa hanna sukayi tashiga tayi wanka sannan tayi drying jikinta,"   LBV makeover suka fara tsantsarata."
 Zuwa 7:45 angana makeup, "
Alokacin idan kaga *hanna*  yadda kasan yar tsana tsabar kyau,"
 Wata farin wedding gown *hanna* tasa k'asanta tun daga nesa yakejan k'asa. "
V head aka d'aura mata sannan aka yafa mata farin stone net." da farin hill asalin mai tsinin jikinsa stones ne yadda kasan diamond. "
  Sunhanallah kaso kaga *hanna* awannan shigar. "
Yadda kasan princess piona." Su hameeda kuwa da sauran frnd natta, "
   Wani pink d'in material mai tsadan gaske sukasa da farin head sannan kuma da farin takalmi hill."
Kowacce ta riqe yanonon farin gyale ahanunnunta, "
Gabaki d'aya k'awayenta Su 6 ne Sai abin yabada kala."
 8 dai-dai akace Su fito ana k'ofar shashin basu d'auki lokacii wajan fitowa ba dan sungama shiri."
  Hanna sukasa atsakiya zuwa waje Suna fita hasken solar ya dallare Su,"
Alokacin suka k'ara bada kala,"
  Motocii suka ganii guda talatinn da d'aya cuss, "
15 agaba 15 abaya Sai kuma 1 atsakiya fara soll ferarri mai bak'in tinted, Su kuma sauran duka bak'ake ne wulik hadda tinted gabaki d'ayansu iri d'aya ne rang rover,"
Direct farin ferarri d'in suka nufa, dan sunsan cewa ita ce ta amarya ko ba'a fad'a ba."
  Dai-dai motan sukaje sukaja suka tsaya, "
Bud'e driver seat akayi captain ahmed ne yasha milk d'in shadda ne ajikinsa yayi kyau sosai,"
Yana zuwa yabud'e mata motar yayi alamu da hannunsa alamun ta shiga motar ya sunkaya kai alamu girmama wa. "
  Cikin takun isa wanda takalmin k'ofar tane yadameta yasata tafiyar wanda hakan yazama kamarna k'asaita."
   Shiga motar tayi yayinda MG ya lumshe idanuwa sakamakon  Wani daddad'an kamshi daya ziyarceshi, "
  Itama hakanne awajanta kamshi ne mai sanyi ya ziyarceta irin kamshin datajii a wannan d'akin amma na Yanzu dabanne."
   Tana shiga c. Ahmad yarufe kofa koda tad'an juya gefe kawai ta tsincii MG na kallonta ko kiftawa bayayi. "
Saurin d'auke kanta tayi dan ita idan aka barta Sai tace da aljani tayi gamo."
Tarasa Wani irin kyau yakeda shi. "
Kyawunshi har Wani fusgarta yakeyi Cikin ladabi da jin kunyarsa ta gaidashi bai amsaba saima kafeta da ido dayayi."
Jin shiru yasata d'agowa ta kalleshi nanma caraff idanuwansu ya had'e, "
Wasu irin abubuwa taganii Cikin kwayar idanuwansa."
  Yanzu ma farar shadda ce kall ajikinsa har tafii ta d'azu d'aukan ido, "
Farin talami da hula Sai farin diamond links,"
Gaskiya MG maikyqune. "
Sunkuayarda kanta tayi tana wasa da yatsunta aranta tana tunanin maiyasa MG yake sonta,"
Nafarko itaba kyawun Azo agani ba. "
Ahaka tayi ta tunani har suka shirya aka tashi motar da sauran motocin."
Ahaka suka isa bbu wanda yacewa d'an uwansa Wani abuu."
Hafsat kuwa motar captain bilal tashiga Suna tafiya Suna soyewa dan yanzu abukam yayi nisa."
Soyayyarsu sukeyi. "
  Amira kuma yaya jalal najiranta dan tun d'azu yake kiranta,"
Duk da cewa bai fad'a mata komai ba amma tafahimcii cewa Yana sonta kuma Itama tasan tana sonsa kawai jiransa take ya furta bazata 6ata lokacii ba zata amincee. "
  Tsayuwar motar da sukajii ya tabbatar musu da an iso wajan."

To be continued

Ur's
      *z33yyb3rw3r*

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

   Wannan shafii sadaukarwane ga masoyana  *Asma'u A muhammad*
  Inasonki sosai kamar yanda kike sona,"
Ina jin dad'in yanda kike bibiyar labarina,"

  *Khadeeja*  hak'ika ke masoyiyar kwarai ce inasonki ina alfaharii dake, "
Kisani ko acikin masoyana ke ta daban ce."
 Asma'u n Khadeeja gaskiya ina sonku irin sosai d'innan."
Karku damu ana mugun tare."
  *I heart ❤ u girls."*
 

Page 58

* Zaune suke acikin wajen sunkai kimanin shida,"
   Cikin muryar k'aguwa da damuwa d'ayan yace duk rintsi musan yanda za'ayi yau mu kashe Shi. "
   Idan ba haka bafa muna kallo kamar ya sake ne amma tabbas zai dawo kanmu."
  D'ayanne ya nisa yace senator inaso ka fahimceni duk yanda kake tunani tsaron wajannan yawuce haka. "
Duk iya dabar barunmu da k'ok'arinmu hakan bazaisa musamu Wani k'ofa ba,"
Tun jiya ake tsaron hotel d'in bbu mai shigarsa balle kuma yau dazai shiga kuyi tunani mana. "
  Bafa k'aramin mutumi bane da zamu samu damar kasheshi dasauki."
  Ko wancan karanma dan daniel ya kasance d'aya daga Cikin sojojin chief ne yasa muka samu damar kai masa harii. "
   Karfa ku manta awancan lokaciin munyi amfani da tsanar dake Cikin zuciyar daniel ne muka tursaasa Shi ya yarda harya rasa rayuwarsa,"
To yanzu kuma mushkila ke d'an za'asamu asirinmu ya tonuu."
   Mujura lokacii amma ba wannan ba. "
   Amma acikinku duk wanda yace ba hakaba toh tabbas saidai yayi Shi kad'ai idan kuma dukanku zakuyi toni bbu hanuna."
   Kai barima nafito fili nagaya muku nikam nagajii da wannan shurmen,"
  Laipy ne mun aikatashi mezai hana mu kar6i hukun cinmu?. "
Musan cewa munyi ba dai-dai ba."
Nigabaki d'aya ma wallhy ina danasanin biye muku danayi muka cucii al'umma,"
   Wallhy Allah bazai ta6a barinmu ba."
   Allah sayya sakawa way'anda muka zalunta,"
   gwara mu kar6i hukuncin mu tun agidan duniya,"
   Bansan lokacindaa na'aikata wannan abuu mai yashiga kaina ba, "
Gabaki d'aya namanta cewa bayin Allah muke zalunta namanta cewa komai daren dad'ewa Allah zaimusu sakayya."
  Hawaye nagani afuskar sa,"
  Yace zanje zancii gaba da rok'on gafarar ubangiji kafin gaskiya ta fito."
 Danni yanzu nafii buk'atar hukuncii dai-dai da abinda na aikata. "
  Tashi yayi yace nidai kunga tafiyata,".
  Amma yakamata kuyi shawara ya fad'a sannan ya sa Kai zai fice. "
   D'ayanne wanda najii ankira da senator yace minister minister yaya zakqmaanq haka kafasan irin hukuncin dake kanmu."
   Fucewa yayi bai saurare Su ba. "
  Cheif ne yace haba senator Ahmadu yaya zakq d'aga hanklinka mubashi nanda kwana biyu idan yak'i Sai atura akawar dashi, shine zaifii mana sauk'ii kawai,"
  Nisawa wanda aka kira da alhaji sulaiman yayi sannan yace tun farkon sanda nacewa, senator kada asa minister acikin har kallan nan gashi Yana shirin kawo mana matsala. "
Kokad'an banso yashiga ba dan yanada saurin karaya."
   Senator ne yace yanzudai kawai shawarar chief zamubii, "
  Kawrda shid'in shine rufin asirinmu."
 Ahaka suka tashi kan gobe zasu kirashi sujii mai ya yanke, "
   Dandai bazassu lamunci yatona musu asiri ba."
   Ahaka suka tashi daga meeting d'in,
Kowa ransa a6ace."

 *Royal tropicana suit hotel*

A  Dai-dai nan motociin suka tsaya,"
Kai tundaga wajen hotel d'in zakasan ana bikin manya,"
 Captain Ahmad ne ya Bud'e masa k'ofa sannan shikuma MG ya zagaya ya Bud'e wa *hanna*  k'ofa, "
  Hannuwansa yasa mata ta kama ta futo,"
  Sai tayi kamar bata ganii ba da dafa kof'ar motan da front seat,
 ta zuro k'afafunta ta fito. "
   Dakyar tasamu ta tsaya dai-dai dan tsinin takalmin yayi tsini dayawa."
  Fita k'awayen amarya da abokan ango suka matso suka."
   Jerawa sukayi abin gwanin ba sha'awa. "
  Afeeya ne tafito daga Cikin wajen tsaya tayi turuss ganin Su seprated."
   Kamo hannun MG tayi sannan takamo ba *hanna* tahad'a Su waje d'aya, "
  Wani irin shock sukayi dan wannan ne first tym na *hanna* data ta ta6a riqe hannun MG fatanshi is soft n silk *hanna* sanda ta lumshe idanuwanta tsabar irin yanda taji hannunsa kamar tissue."
   Shima MG hakanne yake anasa wajen dauriya kawai yayi ya riqe hannunta. "
  Ahaka suka fara tafiya Cikin takun angwaye da amare komai na k'asaita."
   Ahaka suna tafiya masu pics vedio harda y'an jarida, "
  Flash ne kawai ke haske Su tako ina."
  Hasken dayayi yawa ne yasa *hanna* kafafunta suka fara rawa danko kallon hanya sosai batayi. "
    Ganin haka yasa MG yasa hannu yaza gaya awaist d'inta,"
   Batasan lokacin da ta kalleshi dasaurii, ba amma shi ko ajikin sa, hanya kawai yake kallo yacii gaba da tafiyarsa, ita kuma takasa d'auke idanuwanta daaga kansa. "
  Yasan tana kallonsa amma yak'ii juyawa,"
  Sai can tadacii gaba da kallonsa can sunzo shiga event hall d'in yajuyo ya hure mata idanuwa, "
   Lumshesu tayi ta k'ara bud'esu akansa sannan takawar da idanuwanta kunya duk ta isheta."
    Ahaka suka shiga wajan gaskiya ba k'aramin decorating akayiwa wajen ba. "
   Farine soll Sai pink bolb,"
   A haka har suka isa wajan zamansu suka Zauna, "
   Event yayi event Alokacin ummii suka iso,
  Alokacin aka kirasu tsakiyan fili, suka sauko hannunsa mak'ale da nata ba k'aramin dad'ii ummii tajiba ganinsu haka,"
Alokacin su kilishi umma da sauran iyaye Suna tsaye afilin. "
    Sanda sukazo dabb Su sannan *hanna* tatsuguna k'asa tana gaidasu yayinda MG shima yabita ya tsugunna."
   Shima Yana gaishesu abin yamatuk'ar k'ayatar da duk mutanen dake wajan." Hakan yanuna musu alamomi dayawa."
  Nafarko tanuna mutane yarbiyanta gashi na biyu yanda ta nuna wa mutane cewa samun mace tagari Yana daga Cikin abin da yakesa namiji gyara halayensa. "
   Yanzu kuduba yanda MG baiyi niyar tsugunawa ba amma ganin tayi hakan yasa yayi."
Allah yasa muzama mata nagarii. "
Ameen
   Kasancewar tsugunawa wajan gaida nagaba ak'asar hausa abune maikyau wanda hakan ana samunsa ga yaro mai tarbiya yasa mahaifansu jin dad'ii da alfaharii da yaransu,"
   Dad'ii ne yacika ummii  na irin girmamawa da diyansu suka basu. "
  Sa hannu tayi ta dago Su duka Su biyun sannan ta rungume *hanna* tsam kamar mai shirin maidata ciki,"
Ganin haka kawai MG yafarqyi musu liqi da 1000 dubu dubu sabii, "
  Sannan labba ma tshigo itada afeeya suka jona,"
  A sauran dangima sukabi bayansu, "
  Kowa liqi yake musu,"
  Dakyar ummii tasaketa, Itama tahau yimata liqi,"
Waje yayi waje biki yayi biki. "
   Manyan mutane sun hallarq,"
   Can na hango y'an BIBIYATA AKEYI FANS, hardasu ameen, aishatu g sabo, aisha ayuba, mmn hassan, maman waleed, Su asm'aul husna,
  Su bintu abacha kam ba kantq tasa plate agaba Sai taga k'arshensa, "
   Sai kiyi saurii dan ummu sudais na jirankine ita takawa takesonyi,"
    Su momy bayo kam andad'e afilin rawa Itada saudat."
   Kunsan bikin na manya ne Can na hango murjanatu gimbiya liqi kawai takeyi, "
   Maimunat da hajara ya'u aliyu haka kuka iya rawa😳
   Maman twinx madai ba'abarta abaya ba dan tura twinx gefe tayi tashiga hidima."
   *Hanna*  na godiya kuma tajii dad'inn halartar bikinta da kukayi😃."

   Intisar idan ka ganta Sai kace aljana dan Wani irin kyau tayi. "
  Batafin 10 minute bata wuce gaban MG ba tanayi tana karai raya,"
   Amira kuwa anmak'ale itada ya jalal Sai soyewa sukeyi. "
   Balle hafsat da abuu yayi nisa."
   Tare da yaya jalal suka shigo fili suka yi barnar dukiya, yaya jalal yafice ya tafii ita kuma dasu labba hameeda da sauran kawaye rawarsu sukasha *hanna*  tataso har fili tamusu liqi Sai dariya take tana annashuwa amma koda wasa bata yi rawa ba bbu yanda basuyi da itaba dariya kawai take musu tana liqi. "
   Sanda suka gajii kafin suka fita daga filin."
  Nan aka bukacii ganin ango da amarya kawai afilii Nan suka fito. "
  Bbu yanda MG baiyi sutaka ba amma bbu wanda yayi rawa acikinsu."
  Yau anga dunkum d'in amarya da ango banda murmushi bbu abunda sukeyi, "
Amma bbu mai alamun fara rawa."
   MG ne ya bukacii abashi loud speaker, ba Tare da bata lokaciba aka miko masa,
Yajuya yakalli *hanna*  yace. "

 _Kuyi hakurin jina shiru da kukayi jiya amma kubini bashi zuwa dare zan biyaku._

   To be continued

Ur's

    *Z33yyb3rw3r*

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )



Page 59

*
Matsowa yayi dabb da ita har sunajin numfashin juna yace, "
   I love u"
I love u with every single blinks of my eye's, nd every secound of my love."
  Ido *hanna*  tak'ura masa shikuma yasa hannunsa yakamo nata Yana murzawa ahanakali sannan idanuwansu na sarke Cikin  na juna."
  Yacigaba da cewa."
I vow To be loyal, to be honest and truthfull with u at good n bad times."
   Shiru yayi na y'an secound Yana murza hannunta."
   Wanda hakanne yafaru ga duk hall d'in kowa Shiru yayi Yana kallonsu Yana sauraronsu, "
  Barin y'an matan they wsh da sune *hanna* ."
   Ahaka yacigaba da magana,"
 Matse hannun  *hanna* yayi dake Cikin hannunsa sannan yace, "
 And hopely I will try to be d best husband for you my wife,"
  And best father for our children nd best grandfather for our grand children. "
  Dariya ne sosai yakama *hanna* saita rufe bakinta,"
  Da d'ayan hannunta d'ayan kuma nacikin na MG." 
   Yanda take dariyar da yanda yatsaya kallonta Cikin nishad'ii, "
  Ya k'ara bawa mutanen wajan sha'awa."
   *Hanna*  ne tace an I promise to take gud care of you," am going to be ur best And truthfull frnd,"
  D'aga masa gira d'aya tayi sannan tace, "
  U knw truthfull frnd are alway's hard to find,"
  But am gonna be dat truthfull for u dear,"
 Am going to be ur 6ter, frnd, "
  Am gonna take good care of u just like a little baby."
   Dariya abun yabashi Sanda ya d'an dara. "
  Yazo dai-dai kunnenta yace keep ur promise."
   Afili ta furta yes,"
Am going to be d most amazing wife ever. "
    Uhummm abunda MG ya fad'a kenan."
  Kamar rad'a yanda bbu maijii *hanna* tace dats all. "
   D'aga kafata yayi shima ahankalin yace not bad."
    Cikin D'aga murya kuma yace I vow to make u da happiest women on earth."
   I will make sure dat every girl is jealous of u, "
   Yafad'a Yana jijjaga hannunta."
   Tsayawa kallonsa tayi bata ko blinking idanuwan ta."
  D'an sunkuyowa yayi ya hure mata idanuwanta."
  Lumshesu tayi sannan ta bud'esu."
  Muje toh Yafad'a ahankalii. "
  Okkk. Ai bata gama rufe baki ba suka farajin ruwan kud'ii akansu badaga y'an uwansa da y'an uwanta ba abokanansa kam ba'a magana da nata kawayen."
  Hameeda ne ta sunkuyo dai-dai kunnen Amira tace dubii *hanna* munafuka kamar ba itane d'azu tadamu mutane da kuka ba gashi yanzu tasake tana zuba love, "
  Uhmm Amira tace sannan tak'ara cewa ke beb abunnefa bbu sauk'ii."
   Tsaki Hameeda taja tace ainaga alamu kema kwanan nan kinfara shigane."
  Amira bata k'ara kulata ba dan tasan idan adah tayiwa tsiya ma masoya yanzukam bazatayi ba. "
  Intisar nacan gefe banda kuka bbu abunda takeyi,"
   Wani irin kishi ne yake tunurnuk'anta,"
  Zafii takejii acikin zuciyarta tadaga bbu wanda yasan tanayi kawai saita fice tazarii motanta tayi gida. "
   Su affan Sai kud'ii kawai yake zubawa kamar baisan zafinsu ba."
   Dama duk dangin MG wannan ranar suke jira shiyasa suke shagalinsu, "
  Sosai biki yake buguwa *hanna* jitayi kamar tayi kuka dangajiya,"
  Basufin 5 minute za'a kirasu fili. "
   Sai 11:00 kafin aka tashi awajen diner d'in, kafin atashi abubuwanda *hanna* ta mallaka basa irguwa."
   Antashi amma ango da amarya bbu halin tafiya dole saisun jira kowa ya watse,"
    MG na kallon yanda *hanna* ta maqale Amira ta k'ii barinta ta motsa ko nanda can itakuma ta matsu taje wajan yaya jalal amma yanzu tasan harya tafii ma. "
   Murmushi kawai yayi ganin yanda *hanna*  take Wani d'ar-d'ar abin saiya bashi dariya."
   Ahaka Sanda suka sallami kowa amma hannunta na maqale dana Amira, "
   Yakasance daga shi Sai guard dinsa," Ahaka sukaje shiga mota, "
  Nanma *hanna* tamqale Amira dole Sai front seat Amira tazauna sukuma Suna baya."
  Ahaka har suka isa bakin shashin d'in da suka dauko Su, "
 Suna sauka amira tafuce da gudu tana saurii ta shiga ta kira yaya jalal."
  Kok'arin fita takeyi yayinda c ahmed ma yafice. "
    Cafko hannunta tajii anyi dasaurii tajuya, tana kallonsa shima kallonta yayi yace"  Ina zakije maraai raice fuska tayi sannan tace bacci nakejii, nikuma banajin bacci Yafad'a kai tsaye."
   To ni ai inajii Tom maimaita abunda kikafad'a d'azu saiki tafii. "
  Zaroo Ido tayi kamar zatayi kuka tace"
   Bacci fa nace maka inajii. "
   Eh  nikuma maimaita abunda kika fad'a nace kiyi."
  Ni ma manta ta fad'a. "
  Daga kafata yayi yace tom kiyita zama anan dama ni bangajii da kallonki ba."
   Ganin tana shirin yin kuka yasa yace ok, jeki kwanta, "
  Harta juya yace bakijii ba,"
  Uhmm tace sannan tajuyo,"
  Light kiss yabata agefen lips d'inta sannan yace saida safe, "
  *Hanna*  daskarewa tayi awajen Sanda ya k'ara maimaitawa sannan tajuya zata fice da saurii."
  Kamo hannunta yayi yace bakin sava guduba wannan rigar yasarda ke zatayi."
    Aikuwa bata kulashi ba tafita, shikuma ya jingina kansa ajikin seat kawai Yana kallonta."
   Koda ta fita tsayawa tayi ta cire takalmanta sannan tatafii dasaurii saurii. "
   Sanda tashiga tarufoo k'ofa sannan tasauke ajiyan zuciya aranta tace lallai ma wannan MG d'in ta shafa gefen lips d'inta kawai Sai ta tsincii kanta dayin murmushi."

   

  _Small is better dan neva_
  _I field my promise_

To be continued

Ur's
     *Z33yyb3rw3r*

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

  *Yi k'ok'ari kazamo nakowa koda kowa baizama naka ba."*

   *Kaji tsoron Allah alokacin da mutane sukejin tsoronka."*

    *Kaji tsoron Addu'r wanda aka xalumta."*

  *Kayi afuwa ma wanda yacuceka domin Allah nasan masu afuwa."*
   
      *Nasiha ce*

================

 _Gaskiya *Asmy b aliyu*  littafinki na wata rana yayi irin totally d'innan fa nake gayamiki,   kawai yafito need need irin bocally d'innan, "     shiyasa nake karantashi Royally."    sannu da k'ok'ari Allah Yak'ara basiira."   muna jirankii asabon buk d'inki. "_
  ILYSM❤
 
================

_Tabbas *SADNAF*  ke mai k'ok'ari ce wajen fad'akarwa aduk rubutunki Allah yakaremu daga sharrin grp,"_
  _Gaskiya kin fad'akar kin wa'azantar,"   Allah Yak'ara miki basira,"_
_Allah yamiki albarka duk wani abunda yakeda sharri kina k'ok'arin tunasar damu CIKIN rubutunki. "   more grease to ur shining elbow."_

Page 60

*
   Zagaya d'aki yakeyi yaje yadawo."
 Yak'ara zuwa yadawo, sanyin ac ne yake ratsa ko ina ad'akin, amma kuma gumii yakeyi. "
  Haajiya suwaiba dake kwance, ganin mijinta na zirga-zirga duk yanda yanda taso tq jure abun yafaskara," bata ta6a kallonsa cikin tashin hankali ba irinna wannan karan, "
  Dan dai duk damuwa bata hanashi bacci."
  Tashi tayi tadafashi tace, "
Baban mufeedat lapiya naganka cikin wannan yanayi?"
  Yanzu k'arfe 12:35pm darene amma kakasa bacci,"
  Idan da wata matsala kafad'in mana aisai muyi tamaka add'u'a kokuma muyi sallah cikin darennann, mu roki gafara awajen ubangiji, "
  Kai da kanka kake tunasar damu iyalenka, cewa bbu wani abunda yafii k'arfinn Allah."
  Ganin yayi shiru baice komai bane yasa tacigaba da cewa ni idanma aikin minister d'in nanne kawai Kayi resining, wallhy tunda kahau mulkinnan samun nutsuwa ya k'auracex  maka. "
  Da mamakinta
Gani tayi yajuyao ya riqe hannunta yazaunar da ita bakin gado,"
   Shafo fuskarta yayi ya ce je kikiramun karimah ad'qkinta akwai zancenda zamuyi daku, "
   Tashi tayi tanufii d'akinta," tasan ayanzu kotaje shashin karima ta kulle amma tasan batayi bacci ba, wayarta abud'e zata samu. "
  Wyarta tad'auka tayi dialing numb d'in da aka rubuta habibty, "
  Ana d'auka najii tace ziko d'akin babanku yanson magana dake."
  Gaban karimah ne yafad'ii tunda take da mahaifinsu bai ta6a kiranta a irin wannan lokacin ba. "
Ahaka jiki bbu kwarii tatshi tanufii shashin babnsu."
   Da sallama tashiga d'akin dukansu suka amsa mata, kusada mahaifiyarta tazauna tayi musu sannu duka suka amsa. "
  Sanda tazauna nak'are mata kallo sosai sai alokacin na hangii tsananin kama dasukeyi da mahaifiyarta,"
   Farace doguwa tanadakyau sosai. "

  Gyara zama minister yayi ya fuskancii iyalansa sannan yace,"
Kugafarcenii tabbas nasan abun da zan fad'a bazai muku dad'ii ba, amma kuma yakamata infad'a muku. "
 Shekara d'aya da watanni d suka shud'e,"
  Ina office, "
Sectery yakirani kam cewa inada visitor's ban d'auki lokacii ba kasancewa yasanar danii way'anda keson ganina band'auki lokacii ba nace su shigo duk da cewa abun yabani mamaki."
   Senator ne shida shugaban y'an kasuwa sukazo nemana, "
   Cikin mutumcii da karramawa muka gaisa tareda y'an barkwancii da baza'a rasaba,"
Nan suka zauna Senator ke sanar danii munada muhimminyar maganane, "
  Tom alokacin ban fahimcii komai ba,"
  Kawai dai nad'auka kan wani siyasa ne. "
Munyanke shawara akan zqmu had'u da su a guest house na Senator."
   Anan muka had'u alokacin naga ashe munada yawa wanda za'ayi meeting d'in. "
Ganinsu ahaka ya tabbatar mun cewa ba abin alkhairy bane,"
  Koda nazauna suka fad'amun buktar su, da farko nak'ii amincewa,"
  Kan cewa zan aikata abunda suka bik'ata, "
  Amma Daga baya idanuwana suka rufe kiriff da ganin kud'ii na aikata sa6on Allah."
  Tun kafin yafad'ii lqifinda ya aikata, karima tafara hawaye dan ta tabbata ba abuu ma dad'inn jii bane mahaifinta ya aikata. "
   Hajiya suwaiba da duk itama zuciyarta ta karye tace,"
  Abban mufeedat wani irin abubuwane haka ka aikata? "
  Nisawa yayi yace munshigo da gur6ataccen maganii wanda ak'allah mutane samada d'arii biyu suka mutu ta dalilin shan wannan maganii."
    Dagowa yayi ya kalli iyalansa wanda duk hankalinsu atashe yake dan kukama sukeyi yace." Wallhy da hannuna danni da kaina nasa hannu atakardar muka shigo da maganganuwan. "
  Idan baku manta ba shekara d'aya data wuce anyi ta mutuwa wanda aka alaqanta hakan da annoba,"
  Mutane darii biyu sun rasa rqyukansu, samada darii biyu sun nakashe. "
   Kuka Hajiya suwaiba takeyi tana dukan k'irjinsa tana cewa Abban mufeedat meyasa?"
Meyasa bakayi tunanin bayin Allah ba awannan lokacii?"
Adah nad'auka cewa mujina adalin shugabane ashe bansan cewa ina zaune da wanda baya tausayin talakawansa bane. "
  Rungumeta yayi yana rarrshinta Kuka kawai takeyi banda karima da itama har shid'ewa takeyi dan Kuka."
    Share hawaye yayi yace suwaiba san zuciya ne yasa, "
  Wata k'asace suka karyar mana da farshin maganin Kan sunyishi ba ka'iida ba,"
  Amma kuma abun mamakin Anan shine sukuma y'an kasar da suka sayar mana, suma sun sayar ak'asarsu amma kuma hakan bata faruu ba. "
  Maganii baya musu amfanii amma bai kashee wani kokuma naksar da wani ba."

  Alokacinne nashiga buncike, "
  Abinciken da nayi ya nunamin cewa amfanii sukayi da jinin al'ummar suakcii za6e."
  Sannan Abinciken nagano cewa mu biyu aka rufe bamusanda wannan al'amarii ba. "
  Ganin mutuwar tayi yawa yasa shugaban sojjoji na k'asa da k'asa wannan yaron wanda akeyin bikinsa,"
  Yashiga buncike ton duk yagano cewa dasa hannu aciki kuma yasamu evidence, "
  Wanda alokacii d'aya zaigamo masu hanuu,".
  Hakan yazao kunnemu ne daga wajen shugaban sojjoji na k'asar Nan."
   Dan duk wani abunda zqmu yin da hannunsa aciki. "
 Sannan kuma yashaida mana cewa yagano da hannun shugaban kasuwa da custome aciki,"
  Kuma yatabbata zai iya gano wa cewa da hannunmu aciki. "
   Bamusan maiya faruba yayi tafiya na y'an month,"
 Acan dubai muka shurya kasheshi Allah baiyiba. "
And yaban yadawo na wasu month muke tunanin sake Kai masa harii."
    Amma nafuto na fad'a musu cewa bazan iyaba, "
  Dan yanzu nikaina nafii buk'atar hukuncii fiyeda komai."
  Nafii buk'atar ayiwa way'anda na zalumta sakayya, "
 Ina tsoron gamuwata da Allah."  tashi yayi yabud'e wasu jakka Sannan yad'auko duk takardunda yake ciki ya miqa musu, "
 Da kunnena najii suna cewa wai zasu kasheni gwamma sikasheni Tun yansu,"
  Su d'auke duk wani zunubinda nake dashi akansu. "
  Fargabata d'aya kada suce zasu ta6amun iyalina kuma nasan zasuyi k'akarin aikata hakan,"
   Ki dauki y'ay'ankii kuje kada ku zauna."
  Inada wani gida acan gandun albasa, bansaya da sunana ba ku je can bbu mai sanin cewa kuna raye, "
  Kungq mufeedat bata k'asa idanna ce," Kuje wajanta za'agane cewa kunfita daga k'asar dan kunsan ba kananun mutane bane. "
  Nabiyu gashi duk wata dukiyar dana mallaka tana cikin nan da takarduna da information na bankuna,"
  Kada wani acikinku yasake amfanii da atm d'insa ga tsaban kudii acikin wancan jakar kuyita amfanii dashi, harsai randa kukajii cewa ankamasu Sannan kufito Kuyi rayuwarku Kamar kowa. "
   Kuka hajiya suwaiba takeyi sosai tace wallhy abban mufeedat bazan iya tafiya nabarka ba,"
  Bazan iyaba idanma mutuwane nafii buk'atar namutu kusada  mijina. "
   Girgiza matakai yakeyi yana a'a hajiya kitafii da yara kinga kinada k'ananun yara,"
  D'gowa tayi ta kalli karima tace karima Ki riqe k'annanki da kyau dan Allah Ki musu tarbiya mai kyau, "
  Idan Allah yasa kwanan mu yak'are nida mahaifinki kuyita manq addu'a." bayadda mahaifin karima baiyiba akan hajiya sawaiba tabisu ba amma takii, "
  Jakar kud'in yad'auka kirar dana ta kardiun ya nafii bayan gidansa yasa abayan wata mota vibe."
  Hajiya suwaiba kuma ta shiryawa d'iyanta kayansu a trolyn dukansu."
   Itama takai musu motan, "
Ahaka tatashi abida dake bacci wanda bazata wuce 17 ba sai dan sa'ad dan 14.  Da kuma y'an biyu hassana da usaina,"
  Sai autansu kabir 7yr's, "
  Karima tana Kuka Kamar ranta zaifita iyayenta suka turata amota,"
  Duk sauran basusan maiyake faruwa ba, amma suma Kuka kawai sukeyii iyayen sukabii d'aya bayan d'aya suna rungumewa suna yiwa y'ay'ansu addu'ar nasara. "
 Sauran yaranma duk Kuka sukeyii banda kabir dayake bacci."
  Minister ne ya leqa ta window yabata wani photo yace, ba lallai abinda nashirya yatafii dai-dai ba, "
Amma duk lokacin da Kuka shiga matsala kinemi tajikin pic d'innan inada tabbacin zata taimakeku."
  Kada Ki tada motar harsai kinga kirana yashiga wayarki. "

Ahaka suna kallo babanta yawuce yatafii ta baban gate nan y'an sandan da suke tsaronsa suka takemasa baya."
 yana futa kuwa yaga abinda yake zato mutane ne acikin mota har uku agaban gidan. "
  D'aya ya dagwa yawa yakira sauran akan suzo ko za'asamu matsala ga Minister nan tanan k'ofar."
Aikuwa duka suka tattaro zuwa nan alokacin Minister yadanna wayarsa dake aljihu yakira diyarsa, "
Tana kallon kiran mahaifinsa ta tada motar ahankali tafice tabar anguwar."

Shikuma sanda yatabbatr tabar anguwar ya juya yakoma, "
Gabaki d'aya kansu yad'aure ganin yakoma."
Yana shiga gida yakira senator, "
 Senator na d'auka yace dama nasan zaga sauko ma."
Dariya Minister yayi yace kakarancenii abaibai, "
Kasa tsaro ak'ofar gidana kana tinani zan gudu ko,
To Allah yafiaka, yana fad'in haka ya katse kiran."

=============== wannan rana takasance ranar da mutane dayawa bazasu manceta ba, wasu takasance musu ranar farinciki wasu kuma takasance na bak'in  ciki."
 Ranar intisar kwana  tayi bata runtsa ba tsabar bak'in ciki da kishi. "
  MG kuwa shima hakane takasance anasa wajan amma shi saba'anin haka,"
Tsantsar farinciki da nishad'ii yake ciki kokad'an baisamu bacci ba sai 3:30 yana nafil fili na yiwa Allah godiya, nacika masa burinsa."
  Sai 3:30 yasamu ya kwanta bacci yayi wanda rabonsa da bacci mai da d'in haka shekara goma tunda yad'aura idonsa akan *hanna*   ko kuma ince bai taba bacci mai nishad'in haka ba. "
   Sanda yamakara asallah,  sai 6:00am kafinnan yafarka yayi sallah duk da haka bawqi baccin ya isheshi bane yana idarda sallah ya kwanta bacci."
Dan jinsa yakeyi fayau Kamar wanda aka d'auke masa nauyii. "
   Itakuwa *hanna* anata wajen bazaka iya bambamce farinciki take cikiba ko saba'anin haka, amma dai tana cikin kewar mahaifanta na gaske,"
  Dakyar bacci yad'auketa."
  Wajan minister kuwa da hajiya sadiya kwana sukayi nafil fili, sunata zuba ido suga abinda zai biyo baya amma shiru har garii ya waye bbu wanda ya runtsa."
   Sai karima da sun isa gidan tasa, yan kannenta dasuke bacci agaba kuka kawai takeyi, "
  Ahaka takwana bata ko runtsa ba,"
Ahaka abida ma ta kwana tana kallon yayarta, batasan mai yakeyi damunta ba, "
   Tatambayeta iya tambaya amma bbu amsa haka tazauna tazuba mata ido."
  Kawai suka kwana bbu bacci. "

  Iya sauka anyiwa Su *hanna*  sauka, da safe abincii kala kala aka kawo musu na karyawa."
   Sai 9 MG yatshi
Haka kawai yaji yanson kallon *hanna*  kiran labba yayi ta dauka, gaidashi tayi ya amsa kawai sayya fara kame kame, "
 Can kuma yadake yace,"
  Inason ganinta ne Inason zan mata magana, "
  Dariya labba ta kumshe tace yaya yareema waye ita kuma," tsaki yaja yace *hanna* adak'ile, "
  Yaya kakira wayanta mana."
Bazan kiraba yace atakaice, Ki kawota ina garden ta baya kufito ta k'ofar baya."
   Yana fad'in haka ya katse wayar, "
Ad'aki tasamu *hanna* . Nazaune abakin gado sungama waya da mama kenan,"
Kamo hannunta tayi tace zo kiji, "
 Injii mene?" *hanna* tatambaya bata jira amsar taba tacigaba da janta, "
  Wata k'ofa ta bud'e acewar *hanna*  wannan k'ofar d'aki ne amma kawai taga, shuke shuke awajan,"
  Abinda *hanna*  ke matuk'ar so yasq bata kara tambayar ina zasu ba tabita. "
  Ganinsa yana nufosu yasa labba juyawa,"
Ita *hanna*  batasanna tajuya ba, "
  Ya iso ya dad'e abayanta batasanma yazo ba,"
  Kawai jitayi ankamo waist d'inta harta dakar kare zata kwala ihu yajuyo da ita suka kalli juna,"
  Armless shirt ne ajikinza sai 3quater na army,"
   Runtse idanuwanta tayi Ganinsa da singlet abin ba k'aramun dariya yabashi ba yanda ta tamke idanuwanta Kamar taga dodo."
  K'akarin kwacewa tafarayi, "
  Amma takasa saima k'ara matseta dayayi Kamar zatayi kuma tace,"
  Dan Allah kasakenii bbu musu yasaketa,"
 Taja da baya Sannan tace ina kwana, "
  Bai amsaba sai da ya zauna awata kujera dake wajen yace zoki zauna bbu musu tazo ta zauna,"
  Kwanciya yayi akan cinyoyinta ya lumshe idanuwansa Kamar mai yin bacci. "
  Ad'arare take amma ganin ya rufe idanuwansa hakan bai hanata kare masa kallo ba."
   Kallonsa takeyi sosai wanda ita kanta batasan ta shagala akallonsa hakaba. "
  Aranta tana jinjina kyau irinna MG, tasan duk da cewa ita d'iya macece amma kyawunta ko k'ofar nasa bai kamaba."
  Ayadda take kallon  labba tafito suffar larabawa sakk amma MG yafita kyau. "
   Ta shagala akallonsa muryarsa yadwo da ita Daga tunajinta jin yanacewa,"
  Sweery kinsan mene? "
  Dubanta takai gun fuskar sa haryanzu still arufe,"
   Girgiza Kai tayi tace A'a,"
  Gyara zaman kansa yayi akan cinyarta yace, "
 Cinyanki na da dad'in kwanciya jinakeyi Kamar nakoma bacci akai."
Gabaki d'aya maganarsa kunya tabata sai ta kasa amsa masa tace umm kawai, "
  Nayi bacci?" ya tambaya, "
  Umm Ta k'ara cewa,"
  Kusan 10 minute kowa yayi shiru, ganin Kamar yayi bacci yasa tafara wasa da gashin kansa wanda gashin yadade yana burgeta, "
  Idonsa biyu jin yanda take wasa da gashin kansa Kamar susa yakejii,"
   D'aga hannunta tayi ta kalli face d'insa still arufe tace bacci, "
  Tukunna yace,"
 Nan kunya takamata duk atunanin ta yayi bacci ne. "
  Tashi yayi yazauna."
Ta kalleshi tace kaga za'ayita nemana bari na tafii,"
  Yi yayi kamar baiji ba Sanda tasake maiamaitawa, Sannan yace Dan wa aka kawoki gudannan? "
 Shiru tayi Kamar batajii ba, yace ashe bakison tafiya tunda bazaki amsa tambayata ba."
  Cikin jin kunya tace Kai, yace toh idan suka tambayeki yanda kike saikice musu ankawoki wajan wanda kike gidan dashi ne."
  Sake baki tayi tana kallonsa, "
Rufe bakin yace mata ta juya ta rufeeshi kiriff, had'eda turo bakinta juyo da ita yayi yace mani kike turawa baki?"
  Tuno ranar daya balle mata baki tayi yasa tayi saurin Girgiza Kai. "
  Ahaka suka zauna kusan 1hour bawani tad'in kirki sukeyi ba amma kuma kowannensu najin dad''in zamansu ahaka."
  Tashi yayi yace Tashi in rakaki y'ar dad'ii miji anzo wajen miji anmanta da mutane najira, "
  Shiru tayi bata bashi amsaba Dan tasan magana yake nema."
   Har sunzo bakin k'ofar tasakai tana niyar shiga yace baki jiba, "
  Juyowa tayi da niyyar jin mai zai fad'a mata kawai saijin bakinta tayi acikin nasa."
  Kissing d'inta yafarayi, duk yanda taso kokuwar kwacewa abun ya faskara. " Dan kanta takahura tabarshi, Sanda yakusan 10 minute kafin yasaketa."
  Yana saketa da gudu tashige kofan,"
Yafii 5 minute kafin ya Iya jan jikinsa yabar wajan. "
  Itakuwa kasa shiga mutane tayi dan ganii takeyi kowa yaganta yasan maiyafaruu."


 K'arfe 4 kowa yagama shirin bud'ar Kai. "
Nan aka fara gudanar da biki,"
Banda algaitu da kalangu bbu abinda yake tashi a fadahh,"   *hanna* tasha alkyabba mai tsadar gaske sai MG shima Tashi shigar tasarauta ne, "
 Ahaka akayi budar Kai aka goma ango yabud'e kan maryar sa."

To be continued
 

Ur's

    *Z33yyb3rw3r*

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

  *Ka/kiyi aikin kirki domin duniya ba matabbata bane*

*Ka/ki guji hassada domin hassada kan Iya kawo gaba tsakanin al umma, Sannan hassada na cinye ayyuka.*


  *Ka/Ki guji shiga hakkin mutane, domin hakan zai Kai ki/Ka ga halaka.*

   *Yiwa dan uwanka kyakkyawan zato, "  domin hakan na Iya sawa kaima wataran amaka kyakkyawan zato*

  *Nasiha ce*

================

  _*Sawwama kawwama*  ina tayaki farincikin kammala buk d'inki na *bani nayi kaina ba*  Allah yabamu damar amfanu da abin alkhairyy dake cikinsa."_
 _Muna jiran sabon buk Allah yataimaka_

   Page 61

*
  Haka aka gama bud'ar Kai lapiya, "
  Kafin atashi daga wajen *hanna* tasamu kyautar mota biyu daga wajen mai nartaba,".
 Sai kuma babbar kyauta daga wajen moddibbo, "
 Kyautar alqur'anii mai girma, da aka sarrafa bayansa da lu'uu lu'uu sosai hanna tajii dad'iin wannan kyautar alqur'anii, dan bayan falala da d'aukaka irinna qur'anii,"
  D'aukar ido yakeyi,"
Gashi bamai girma ba sosai, duk yanda zataje, zata kasance taredashi. "
  Godiya sosai MG yayi, yana jin dad'iin yanda sukeson *hanna* Kamar y'ar uwarsu,"
  Ahaka suka koma shashin da aka sauke Su."
  Sallar magrib sukayi nan kowa yahau shirin komawa, *hanna* batakawo komai aranta ba, dan Batasan cewa yau zasu koma ba, gidan  abba zasu wuce, Sannan gobe dasafe kuma kowa yawuce garinsa."
   Wasu kuyangii ne da jakadai, suka Yi sallama suka shigo, amsa musu akayi, suka tsaya, curko-curko, "
  Can d'aya wanda da'alamu itace shugansu, tace munzo shirya gimbiya ne tafad'a tana rusuna Kai,"
  Wata k'awar *hanna* ne tatashi ta musu iso har d'akin da *hanna* take, "
  Su amira ne azaune sai rud'awa *hanna* ciki sukeyi duk tawani susuce."
Frnd d'insuce tayi sallama tashigo, labba ne tace shikenan anzo, zaro ido *hanna* tayi tace anzo meh?"
Gyaraki mana yau yau d'innan za'a mikaki d'akin mijinkii, dama ahannu kuke,"
D'azu daga cewa zai gayamiki magana sai d aka shafe 1hour bbu ke bbu labarinku. "
  Kama baki amira tayi, tace dama wato d'azu dana nemeta narasa wajansa ttafi." Tabb lallai gwara Tun wurii azo ad'auketa, akqita dan zuwa jimawa zata Iya Kai kanta,"
   Takaicii ne yacika *hanna* takasa cewa komai, dan tasan kota fad'a wani kayan takaiciin zasu k'ara mata."
 Haka sukayita zolayan ta, suka gajii dan kansu suka barta. "
   Nan suka tashi suka fice, sukuma kuyangii da jakadai suka shiga,"
  Ruwan wanka aka had'a mata, mai had'eda sindaren turaruka kala-kala, masu kamshin gaske, "
  Shiga wankan tayi, *hanna* uwar son kamshii, aikuwa ta bingire aband'aki, sanda takai 30 minute kafin tafito,"
Nan suka hau yimata turaruka irinna al'adan gidan sarauta, "
  Kaya tasaka, atampha, dinkin riga da sket, sunkamata dakyar taakeshan lumfashi." Sannan aka rufa mata lifaya,"
  Mai kyau farii kall gezan ya sauko yarufe fuskarta."
Bayan sungama shiryata suka nufii kofa suka fice. "
  Nan k'awayenta da sauran y'an uwanta suka shigo,"
  Fitoda ita sukeyi labba ta bud'e k'ofar, da zata sadasu da shashin, dan wajen ahad'e yake, saidai ginin d'aya benii ne, d'aya kuma plate ne."
  Ginin saman suka nufa da ita nan suka shiga, kowa sai bud'e baki kawai yakeyi dan kyau da tsarii irinna shashin,"
 Kala biyu aka had'a agidan da kalan da yafiso farii call, da kuma kalan pink, wanda *hanna* ke mutuwar so. "
  Falo biyu ne asama da d'akuna biyu, falon farko ne zaka fara shiga," set d'in white funitures ne, hatta paint na falon white ne."
  Sai d'aki a left side na falon, shima d'akin komai white ne,"
Falo na biyu kuma right side na falon zakabi,".
  Saika sauka mata Kala uku Sannan yasadaka da falon."
  Falon ne ke had'e da dining, da kitchen, sai kuma wani room da extra bed room a falon, "
Shikuma wancan saba'anin wancan ne komai pink ne, har paint na Falo d'aki kitchen da dining area duk komai pink ne." Sai sama kuma shima design na falon kusan d'aya ne sandai shi d'akuna biyun marabarsu bbu nisa, "
An then Shikuma bbu kitchen, amma akwai dining coloured na d'akinsa blue da farii ne,"
Har falonma haka, "
 Itakuma ashh da farii."
   Basu tsaya zagaya gidanba suka suka kaita d'akinta suka ajiye akan gado, Can tsakiyar gadon ta k'ule, "
  Sukuna sauran suka fita zagaya gidan,"
  Kowa sai sam barka yakeyiwa wannan gida na *hanna*
Hankalin *hanna* bai k'ara tashi ba, saida taga suna mata sallama suna wucewa, "
  Y'ar karamar hauka tasoyii amma bbu wanda yasaurare ta, haka suka fice,"
  Fitar hafsat amira da hameeda ne yad'aga mata hankali,"
  Sosai Hankalin ta yatashi ta ringa kuka ta kankame amira, wanda amira ita kanta dauriya takeyi,"
  Hafsat ne tana ahare hawaye zata fuce, *hanna* ta cakumo ta, tana kuka tana hava y'ar uwata kada kitafi Ki barnii dan Allah,"
  Amira kasa daurewa tayi kukan dake nukurkusanta ya kwace, "
 Aikuwa yahau rerashi,"
Hameeda da labba ne kawai basayin kuka, dan sunsan cewa Su ba nisa zata musu ba. "
Amma duk da haka hameeda na goge hawaye, dole takanjii zafin rabuwarsu cikin zuciyarta."
  Amira ne tasamu tafice da gudu, tana rairaa kuka. "
  Sai hafsat tabii bayanta, Ahaka suka fice sukabar *hanna* da labba kad'ai, labba nata aikin lallashi."
  Amma *hanna* Kamar zugata akeyii. "
  Sai kusan 9:30.pm MG suka shigo shida abokanan sa daga Falo suka tsaya, tad'ii sukayi har 10:00.pm tacika," Dan shi aganinsa badacewa bane ace abokanai sun shiga d'akin auranka ba, iyakacinsu Su tsaya afalo. "
Shahid ne yakalli hamood yace,"
Kagaya masa cewa gobe zamu wuce fa,"
   Hamood yace, "
Flight na 12:00.am zamu bii."
  Idan kasamu fitowa tom, Idan kuma amarya bata barka kafuto ba shikenan."
MG baice komai ba, Ahaka suka gama zolayarsa suka tashi, "
  Abubakar ne yace, Kai kasanfa cewa k'aramar yarinya, ka aura, sai Kayi ahankali, tunda kazauna kasha tuzurancii,"
  Banda harara bbu abinda MG yabishi dashi. "
  Har bakin k'ofa yarakasu yajuyo zuwa ciki, d'akin *hanna* yanufa direct, tun daga corridor yfara jiyo sheshahkar kukanta,"
 Da sassarfa yak'arasa, "
Yana bud'ewa yaga *labba*  nazaune tana faman lallashi,"
Labba na ganinsa tamike tace alhamdulillahi, "
  Sai kazo ka lallasheta ko Kai tajii naka dan nikam nagajii,"
  Tana fad'in haka taratsa ta gefensa ta wuce."
  Tsayawa yayi Yana kallon *hanna* yace, baice komaiba yajuya ya sauka yarufe k'ofa Sannan yahauro yadawo, "
  Ayanda yabarta Ahaka yasameta,"
Kamshiin turarensa ne ya tavvatar mata daya dawo,"
  Gabanta ne yahau fad'uwa, tattaki yayi har zuwa gaban gadon da take, "
Jin kashin yak'aru kusada ita yasa tasan ya matso kusa,"
  Dan ta cusa kanta cikin cinyoyinta, "
  Zama abakin gadon yayi, yajawota jikinsa Yana bubbuga bayanta, yace baby maiyasa kike kuka hakane?"
  Tun jiya kike abuu d'aya bkya gajiya? "
Yanzu irin kukan da kikayi sai kace wanda aka aura miki dodo?"
  Murgud'a baki tayi aranta tace aikai kafii dodonma,"
  Zame jikinta tayi ta turo baki, "
Tace basu amira bane suka tafii ba."
Murmushi yayi ya lakacii hancinta yace To ba gobe zasu dawo ba. "
  Sauka daga gadon yayi yakamo hannunta yasauk'qr da ita daga kan gadon,"
  Alkyabbar jikinta yasa hannu yacire, "
Tsayawa yayi Yana kallon yanda kayan suka mata kyau."
  Har k'ofar band'aki yarakata yace shiga muyi alwala muyi sallah."
  Turo baki tayi tace ni bana sallah."
  Sake baki yayi Yana kallonta yace, "honey boo bansan k'aryafa yanzu ak'arshen wata muke ba'a tsakiya ba."
   Mamaki ne fall aran *hanna* wanda hakan yagaza b'oyuwa afuskarta sanda ta nuna tayaya akayi yasan date na mensturation nata. "
D'aga kafad'a yayi yace kina mamakine?"
Har doctor da kike ganii, saboda mensturation pain nasani, so Ki shiga kiyi alwala bansan musu."
   Tana tura baki yashiga yayi alwala, tafito shima yashiga, "
  Sallah yajasu raka'a biyu yana zubawa Allah godiya da kirari Sannan yayita musu Addu'r zaman lpy da zuri'a d'ayyiba." Sanda suka idar yatashi yafita, "
  Da bags yadawo Sannan yak'ara fita yad'auko fresh milk a fridge, yaciro plates yazuba musu abincii hanna yitayi Kamar bata ganshi ba, takoma ta kwanta."
  Taso kici abincii yace atakiace nakoshi tace, "
  Idan kika taso gobe zan kaiki gida kiga umma,"
  Mikewa zaune tayi tace promise, "
Yes promise ya fad'a,"
  Tasowa tayi tazauna, fresh milk yafara bata ta karba tasha kusan half Sannan ta ajiye, "
  Abaki yafara bata naman kaza ta k'arba tacii ko musu bbu,"
  Sanda ta daiddaiici ta koshi ta garya masa cizo riqe hannun yayi Yana yarfewa, "
 Itakuma tahad'e rai Kamar ba ita tayi cizon ba,"
  Squra ni ya fad'a mata, "
Nok'e kafad'a tayi tace owh owh kalan karama,"
  Nop bazan rama ba kawai dai inason cin abincii da hannun mata tane,"
  Sharewa tayi yace, kinmanata u promise to take good care of me, jama'a dayawa sunyi witnessing, turo baki tayi ta fara bashi abincii, "
  Sanda yaciika timbinsa tamm,"
 Kafin yaruqe hannunta ya sud'e ya tashi yatttara komai dasukayi mafani dashi yayi waje Sanda yazo daff k'ofa yace Ki shiga kiyi wanka ina dawowa, "
  Bai jira amsar taba yafuce Sanda yasauka k'asa yakai cikin Sannan yadawo yashige d'akinsa."
  Tashi tayi taje dai-dai kofa tace ainii ba kwaduya bace dazakace na k'arayin wanka,
Tana fad'in haka ta datsa Ki ak'ofarta ta koma ciki ta kuskure baki ta wanke hannu, tafito ta kwanta, ko kayan jikinta bata cureba."

To be continued

Ur's
     *Z33yyb3rw3r*

*BIBIYATA AKEYI*         
 _
 _Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
             

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

   *Ka/ki zama mai yafiya, " ga duk wanda ya zalumceka*

 *Ka/ki, zamo mai yarda da kaddara hakan zaisa ki rayu cikin farin cikin,*


   *Ka/ki zama mai yawaita fad'in kalmar Alhmdllhy domin nuna gidiyarki wajan ubangiji.*

   *Ka/ki zama mai yawaita fad'in astagfirullah domin samun yafiyaar ubangiji.*

  *Nasiha ce*
================
  Congratulation *my hajja* for d succesifull complation of ur buk *sab'anin so*  hak'ik'a u tried hard,"
  D buk is insparing,"
Allah yaimaka *my hajja*  u'r such an amazing person, u'r an angel. "
More grease to ur shining elbow."

   Page 62

*
  MG yana shiga d'aki wanka yafarayi sannnan ya fito, sleeping wear's d'insa yasa, ya kwanta akan gado dan tun lokacin da *hanna* ta murd'a key ak'ofarta yaji, " yakusan 30 minute da kwanciya amma yakasa yin bacci,"
  Itakuwa *hanna* baccin ta takeyi, hankali kwance, dan ta tabbata batada fargabar komai ta kulle k'ofar ta."
Tashi yayi yanufi toilet, alwala yad'auro yazo yafara nafil fili yatashi daga sallaya ba saida 12:30 tayi kwanciya yayi baijima ba bacci yad'aukeshi,"
  Kusan k'arfe uku ihun *hanna* ya farkar dashi, da gudu yayi d'akinta gabaki d'aya ya tsorata, "
  Buga k'ofar yakeyi yana ce mata ta bud'e amma *hanna* kuka kawai takeyi."
  Juyaww yayi d'akinsa bedside drawer ya bud'e, spare key's yad'auko, ya nufii d'akinta dashi, "
  Dama MG yanada key na d'akinta,"
  Yabar tane kawai bawai dan dabarata ko wayonta ba. "
Yana bud'ewa ya hangota acan k'arshen gado ta duk'unkune sai faman kuka takeyi."
  Hqwa yayi dasauri yasa hannu yariqota, tana bud'e ido ta kalleshi dasauri tashige jikinsa, "
  Hannuwansa biyu yasa yatallafeta ta baya."
  Yana d'an bubbuga bayanta ahankali."
  Lafewa tayi ajikinsa sai ajiyar zuciya take sauk'ewa,"
   D'agota yayi yana wiping d'in tear's d'in dake fuskanta, sanda yagama yafara tambayanta, maiyafqru? "
  Girgiza kai tayi tace" wasu yarqne sunata kuka suna kiran suna na, "
Kuma daga kallonsu suna cikin wani hali." sannnan wasu mutane biyu suna cewa sunvar amanar y'ay'ansu ahannuna dakai,"
 Jijjiga bayanta yayi yace "  to meye nakukan?"
  Turo baki tayi tace toba yaran bane sunata matsowa jikina ba, "
Sukuma iyayen har jini ne ajikinsu fa."
  Ajiyar zuciya yasauke yace sharrin mafarkine kawai,"
   Sannnan Kuma kin kwanta ba kiyi addu'a ba."
  K'ara turo bakinta tayi tace nifa nayi addu'a, "
  Ok tohm yanzu ki k'arayi ki kwanta,"
A''iina d'in?" ta tambaya tana zaro idoh 😳, anan yafad'q yana k'ok'arin mikewa,"
 Riqe hannunsa tayi gam tace tabb ni gaskiya bazan iya kwana ni d'aya ba."
Da waya saki ki kulle k'ofar ki? "
Ya tambaya,"   turo baki tayi btace komai ba d'aga kafad'a yayi, sannnan yayi hanyar fita, da gudu tazo ta wuceshi, tashige d'akinsa wuff, "
Tsayawa yayi kawai yana kallonta yayi murmushi had'eda Girgiza kai."
   Bin bayanta yayi yasa mu hartayi masauki akan gado,"
Zuwa yayi bakin gadon ya tsaya,"
4 pillow's da Kuma mini pillow su sukafii yawa akan gadon,"
  Jera pillow's tayi atsakani sannnan ta bubbuga gadon tace kwanta anan, " Zama yayi ad'ayan gefen gadon ya ciccire pillow's d'in yace nida gadona sai anyimiun doka?"
 Ki koma d'akinki idan bazaki iya kwana ahaka ba yana fad'in haka ya kwanta."
Ihun kuka tasa tanayi tana shisshure k'afanta duk yanda yasoda tayi shiru amma tak'i, sanda ya mayar da pillow's d'in sannnan tayi shiru. " kwanciyarta tayi batafi 10 minute ba takoma bacci,"
  Shi kuma kallonta yatsayayi, she look's innocent, "
  When she's sleeping,"
   D'an jan hancinta yayi wanda sanda tayi motsi yace but stubborn When she's awake,"
  Ahaka har kusan ten minute baccinta yafara yin nauyii. "
Ahankali take mirginawa cikin bacci batason ma tanayi ba, kawai sai jinta yayi ajikinsa,"
Tad'aura kanta a chest d' insa taci gaba da baccinta, "
Abun dariya yabashi yace y'ar fitina yanzu ina pillow's d'in duk kinbii kin haura kansu,"
  Ahaka shima bacci yad'aukeshi. "

================

  Karimace zaune k'annenta sun sata agaba, akan yunwa sukeji tun jiya bbu Abun da sukacii."
  Kabir kuma yadamesu momynsa, "
 Sauk'inta d'aya ma data kira wayan abbansu tajii yad'auka." suka gaisa nan hankalinta yad'an kwanta, su dukansu sun rame,"
  Abida ne tana kuka tace, gaskiya anty k nikam nagajii, ke baki fad'a mana dalilin kawomu nan ba. "
  Sannnan kin azabtar damu da yunwa ki duba yanda, su hassna ke kuka,"
  Sa'ad kam da baida dariya, yanzu yana kwance cikinsa yana ciwo, "
  Kuka karima tasa tace Abida rashin gayamiki danayi shine, yafii miki saukii kici gaba da addu'a in sha Allahu gobe zanfita ba nemo mana abincii."
  Ahaka tayita lallashin su. "
  Agogon bango ya buga 4:00am na asuba, minister da hajiya suwaiba sunakan sallaya,"
  Basujii shigowa gidanba k'arar murd'a kofa kawai sukajii, "
   Wasu k'artaine suka shigo d'akin,"
Salati su minister sukasa sosai jikin hajiya suwaiba yafara 6ari, "
  Basu tsaya wata wata ba suka miqa masa waya,"
K'ar6a yayi yana jin muryqr senator yayi yana cewa, "
  Shin har yanzu kanakan bakarka?"
 Gurgiza kai minister yayi yace nikam nagane gaskiya yanzu saidai namaka addu'ar shiriya, "
  Dariya senator yayi yace banso kashekaba taurin kanka yaja,"
Kwace wayar wannan k'aton yayi, senator ne yace Ka kasheshi Ka kashe duk iyalansa sannnan ku k'ona gidan, "
  Ahaka sukayiwa minister da hajiya sabuwa yankar rago subhanallhi 😭 sannnan suka bi duk gidan iya bincikensu basu gano kowa ba."     kona gidan sukayiwa gabaki d'aya, "
  Dan dama kafin su shigo sanda suka kashe sauran sojojin, way'anda kuma suka ga kud'ii suka bada k'ofa sunanan."
  Suna gama aikin yak'ira senator awaya yashaida masa bayan shida matarsa basuga kowa ba. "
  Rud'ewa senator yayi Dan yasan minister akwai d'an banzan wayo,"
Yab'oye sune. "
  Wata dabarace ta fad'o masa, yace kajirani yanzu zan turo naka phn numb d'in d'iyarsa kayi tracing,"
  Banso garii yawaye baka gamamun da ahlinsa ba, "
  Bazai ta6a barinsu sutafii batareda Wata shaida ba."

  MG ya farka tun kusan kiran assalatu ba farko yanaso ya shirya yatafii masallaci, amma baison yatshi *hanna*  dake baccinta hankali kwance. " Irin gajiyar da tayi yasata, bacci sosai har batajii kiran sallah ba. "
Ahaka yana gani har akayi sallah aka idar,"
  Sai kusan 6 kafin ta bud'e idanuwanta,"
  Mayarwa tayi ta kulle, "
  Jinta ajikin mutum yasata tashi zaune."
  Har zata fara masifa ganinta a jikinsa, "
  Juyawar da zatayi ne taga filin data barii acan baya har pillow's d'in data jera ta tsalake,"  kunyace takamata, sunna kanta k'asa tayi tace, kayi hqkurii bai kulataba, "
 Cewa yayi kawai kitashi muyi sallah tym ya wuce, tashi tayi taje tad'auro alwala shima haka, nan yajasu sallah,"

Karima na idarda sallah tatashi tafita bataso garii yayi haske gyara tanema musu abincii, "
  Fitanta ta hango wasu mutane na yiwo gidan kuma tabbas bata yarda dasuba, gidan takoma cikin sassarfa da tada kannaneta duka suka yi bayan gidan, da jakkunan takarku dana kud'ii kawai ta iya d'auka su tafa jefawa tabaya sannnan tasamu abunda zasu taka duk ta ingiza kannenta, itama ta samu tahau. "
    Jini duk ya6ata jikinsu Dan sucurity wire's sun yayyaankesu."

  D'akinta ta koma ta k'ara kwanciya sai 7:30 tafarka wanka tayi ta ta yi kwalliya sosai kana ganinta kaga amrya,, gyara d'akinta tayi sannnan tafito da niyyar gyara nasa d'akin, "
  Wata kuyanga tagani tana shirin shiga d'akin, wani irin zafin kishi ne yabai bayeta,"
  Batasan lokacin data daka mata tsawa ba ke ina zakije ta fad'a? "
Jikinta na rawa tajuyo na gaisheta, Allah hucii zuciyarki d'aki zan gyara nasa,"
Ajiyar zuciya tasauke tace kije zan gyara,"
Ba musu ta juya tasauka, ita kuma *hanna*  tak'arasa d'akin ta gyara shi tsabb, ta cika ko ina da turare, tagyara bai d'aki sannnan tafito k'asa tasauka bata ganshi ad'ayan falonva, tawuce d' ayan anan taganshi zaune akujera, "
  Yasa light blue shadda jamfa hannun Yasa links ma light blue,"
  Da sallama tashiga yajuyo yana kallonta yakasa d'auke ido."
  Sanda ta matsa daff dashi sannnan tad'an rusuna tagaidashi amsawa yayi had'eda miqa mata hannu, "
  Bbu musu tariqe hannun yazagayo da ita yazaunar da ita kan kujerar."

To be continued

Ur's
     *z33yyb3rw3r*

*BIBIYATA AKEYI*

_Bismillahirrahmanirrahim_

Writing by
      © _Zaynab Bawa_
 ( _z33iiyyb3rw3r_ )

_Like my page on Facebook :Zaynab BAWA novels_

Followed me on instagram: mhiz_z3iiyyb3rw3r

 

     *Ka/ki girmama mahaifanki, domin mahaifa sune abuu Mai girma kicin rayuwar ki/ka*

*_Ki/ka kasance mai yawan yiwa Manzon Allah SAW salati, domin kaima Allah ya yawaita yimaka salati,_*

 *_Ka/ki kasance mai yafiya alokacin da aka zalunceki/ka, koda kuwa kinada halin ramawa,"_*
 

   *Nasiha ce*

================

 _This page is sincerely dedicated to u my darling, "_
*Aysha hanwa*
_Not 6ter by blood but u'r my 6ter by heart,"_
  *ILYSM❤*
_always heart ❤ u dear._

   Page 63

*
   Zagayo da ita yayi zuwa gabansa, sannan yazaunar da ita akan kujerar da yake zaune,"
   Lallen hannunta yafara bii yana shafawa, bak'aramin kyau Lallen yamasa be. "
  Hannunta ya had'a duka biyun waje d'aya ya sumbata."
  Lumshe idanuwanta tayi ta bud'esu akan sa, "
  K'ura masa ido tayi dan wani irin kyau na musamman taga yamata," kansa bbu hula gashinsa yasha gyara sosai. "  bak'ikirin Har sheki yakeyi,"
  Batasan ta tsareshi da ido ba, kawai jitayi ya hure mata idanuwanta, "  kamshin vanilla flavour ne ke fita daga bakinsa,
  Sunkuyarda kanta tayi tana murmushi," gyara zamansa yayi zuwa kwanciya, d'aura kansa yayi, acinyanta ya Lumshe idanu Kamar maijin bacci."
  Ahankali yafara magana, sweety kitashi ga abincii adining, " dannasan yanzu haka kinajin yunwa amma kike zaune."
  Kallon ikon Allah take masa Kamar bashine ya danneta yakuma hanata tashi ba, Kuma yake zancen abincii adining."
   Sweety ba magana nake miki bane? "  cikin tsiwa da rashin kunya tace, tsuntsu zanyi nqtashi idan baka d'agani ba?"
 Tashi yayi kawai yatsaya yana kallonta,"
   Ni kikeyiwa rashin kunya? "  ya tambaya, kawarda kanta gefe tayi, ciki- ciki yadda bazai jiba tace eh kaid'in,"
   Ai kuwa karaf a kunnenta, "
  Fisgota yayi ta fad'o jikinsa,"
  Bata ankaraba saiji tayi yafara kissing d'inta, da zafi-zafi Wanda kana kallo zakasan tsantsar mugunta yake Mata,"
  Iya k'ok'arii tayi ta kwace amma takasa, "
  Kwalla ne tafara zuba afuskarta, dan ita kad'ai tasan tsanatsan azabar da takeji."
   Sanda yagaji dan kansa yasaketa, yakoma ya lafe akujera yana maida numfashi. "
  Itakuwa Kwalla ne kawai yake, kwarara, dan wani irin zogii da rad'ad'ii lips d'inta ke Mata,".
  Sanda yadawo normal yajuya ya kalleta yace tashi muje kici abinci,"
  Babu musu tamiqe dan batasan mai zai sake aikatawaba, idan tasake masa musu."
     Zuwa tayi ta bud'e wermer's d'in tafara saving d'inshi,"  yana kallo yanda tacika plate da abincii kallonta kawai yakeyi baice mata komai ba, "
  Tea tahad'a masa sannan ta juya da niyyar zuba nata," Kamo hannunta gamm yayi yace, "
  Wa kike tunanin zaicii wannan abincin?"
  Kai tafad'a a dan tsorace, kallonta yakeyi Kamar mai nazarin wani Abu."
  Zaunarda ita yayi agefensa yace, zauna kici abincii danke aka kawo, "
  Kin ga ni ban iya cii ba."
   Kallon mamaki tamasa Wai bai iyacin abincii ba, "
  Dariya ne ta kufce mata aikuwa tashiga yinta bbu kakkautawa,"
  Shikuma yatsaya kallonta, she's unique yafad'a afili, "
 Murmushi yayi yace nabaki mamaki koh."       tace eh, "
  Amma bani kigani ko zancii,"
   Ebowa tayi a spoon takai bakinsa, kawarda Kai yafayi Kamar Angela ta koshi da abincii, "
  Daidaitar bakinsa tayi ta tura masa."
  Sanda sukayi haka sau uku sannan ya cigaba da karban abincinsa yanacii, Sanda yajishi full, ya lakato kumatunta yace, lallai bakida wayo yanzu da ace nace kibani ne bazaki bani ta dad'in rai ba,"
  Turo baki tayi tace wally nima tunda hakane saika ramamin, saika bani,"
  Aikuwa yazauna yabata Sanda tak'oshi sosai tukunna, "
   Tashi duka sukayi da plate d'aya da cup d'aya da Kuma spoon d'aya ahannunta ta nufii kitchen,"
  Binta da kallo yayi yanajin Sonta naratsa duk wani gabbai na jikin sa."
  Tana shiga tatsaya Kallon kitchen d'in, gabaki d'aya yatafii da ita, "
  Ganin ta dad'e ne yasa yabi bayanta,"
Ganinta yayi Sai bud'e ko''inq takeyi,"
  Dariya qbun yqbashi yace Kamar ba itane ta cikaawa mutane kunne da kuka ba, amma yanzu tazaqe tana Kallon kayan."
  Batace komai ba, yak'ara cewa duk kinsa ancika mana gida da pink colour's, Kamar yanda kasa aka cika mana da white ba, tabashi amsa,"
  Fita yayi tabi bayansa, tana cewa Fita zakayi, eh yace atakaice, "
  Marairaice murya tayi tace dan Allah inbiyoka muje mu gaida su ummii,"
  Wani irin dad'ii ne yaratsashi Ganin yanda tanuna muhimmancin iyayensa, "
   D'auko mayafii yace kawai,"
  Up stairs tayi da gudu, ta bud'e wadrope ta D'auko katon hijab da tayi sallah dashi, "
  Har k'asa hijabin, tun tana saukowa yak'ura mata ido bak'amin kyau hijab d'in yamata ba," gashi light blue kalan kayansa, "
  Sanda tazo kusa dashi kawai tadubi hijab d'inta tadubi kayansa, riqe baki tayi," Dariya yayi ya girgiza Kai, "
  Juyawa tayi tace barina canja hijab,"
Riqota yayi yace muje, haka dole yajata, "
  Shashin mai martaba suka fara Zuwa, dan Zuwa 9:00.am zai Fita fadaa."
  Baijira iso ba taga Kai tsaya ya shige, dan dama shi ba'amasa iso baiso,"
  Da sallama suka shiga mai martaba na zaune akujera, yaji dad'in ganinsu sosai addu'a yaringa musu da nasiha."
   Sai suka shiga Shashin kilishi daganan suka shiga na ummii, "
  Ummii Sai murnar ganinsu takeyi labba kuwa tana baccin gajiya."
   Tashi yayi zai Fita ummii tace a'a jira matarka, "
  Sosa Kai yayi yace ummii su Shahid ne zasu wuce inaso na rakasu."
  Murmushi ummii tayi tace ai itama yakamata taje rakasu, dan ta dalilinta sukazo,"
  Kuma nasan yanzu haka basu gana da iyalansu ba, Kuma yakamata ta gansu,"
Ta6ata ummii tayi tace tashi kuje Allah yamuku albarka, da amin ta amsa sannan tafice, "
   Ganin yanda take tafiya yasashi rage saurii, ahankali yanda sojojin dake bayansu da Wanda ke gabansu bazasu jiba tace waikai ko acikin gidanma da sojoji kake yawo?"
  Shima tambayanta yayi Wai bakisan Sunana bane?"
 Daureta yayi bata k'ara cewa komai ba, "
 Wani dan k'aramin flate suka Isa,"
  Da sallma yashiga yasamu sun Gama Shiri suna jiransa ne,"
 Gaidasu *hanna* tayi suka amsa duka suna tsokanarta, wajen matan ta nufa taje suka gaisa, "
  Matan duk da yaransu kabilarsu da Kuma k'asarsu baizo d'qya ba Amma ta fahimcii sunada Sabo, dan d'an zamnsu Har suna ta hira sosai."
  Kar6ar yarinyar matar Shahid tayi, batafii 7month ba wasa takeyiwa yarinyar, matar Shahid tace na fahimcii kinason Yara Allah ybaki masu albarka, akunyace ta amsa ta amin. "
  Tamakar kanwarsu suka d'auketa suka runga bata shawarwarii,"
  Fita rakasu sukayi saida jirginsu yatshi sannan, suka d'auko hanyar dawowa,"
  Ganin *hanna* tayi shiru yasa yacewa driver yasanar da sauran idan sun samii wajan da ake siyarda chocolate su tsaya, "
  *Hanna* tajishi Amma taba kulaba, Hakan dazaiyi bashi zaisa ta manta alkawarin da jiya yamata na kaitq taga umma ba."
  Sanda akazo daidai wajen suka tsaya,"
  Bud'ewa tayi zata Fita, yace Ina zakije?"
  Ai basusan irin chocolate d'in da nakesoba, "
  Sai aka fad'a miki make zansayawa?"
 Idan ba niba waye?" tafad'a had'eda Bud'ewa tafice,"
  Shiga tayi ta za6o chocolate kala-kala wani soja yabiya kud'in suka nufo hanyar Fita, jitayi tabigi mutun gamm,"
Ledan hanjuntane tafad'ii, cewa yarinyar tayi Wanda zata d'an girmii *hanna* kamarda shekara biyu tace kiyi hakiri dan Allah dake *hanna* ne da laipy, "
  Kasa amsawa tayi tatsaya tana kallon *hanna* dan tabatrwa, tana tunano sunanda mahaifinta yagaya mata, *hanna* Kuma ta tsuguna dan d'aukan ledanta, Sanda tajira tad'ago tace mata,"
  Dan Allah sunanki *hanna*? eh *hanna* ta amsa da rashin yarda afuskarta,"
Sannan tace wacece ke? "
  Zancenda akeyi a TV dake manne awajanne yasawa karima fashewa da matsanancin kuka,"
Alokacin *hanna* takai idonta wajan subhanallhi ta furta lokacin aka nuno gawar ministers of health, alullu6e data matarsa, "
  Gidansa yayi gobara, sannan Ana sanarda cikiyar iyalansa ba'asamu gawarsu ba, Kuma ba'agansu ba."
  Juyawa *hanna* tayi idanuwanta taff da Kwalla da  niyyar ficewa, karimane ta cafko hannunta Wanda Hakan yasa d'aya daga cikin sojojin da sukazo da *hanna* ya nufota da niyyar dukanta, "
Hanashi *hanna* tayi tace baiwar Allah sake mun hannu zantafii, muryarta Har na shid'ewa tace, kiyiwa girman Allah kitafii damu, inahh?"😳
 *Hanna* tazaro ido," gidanki dan Allah, dai-dai ta nutsuwarta *hanna* tayi tace intafii daku ku suwa? "
  Nuna mata TV karima tayi tace,"
Mune iyalansa da ake nema, wallahy ba gobara bane kashesu akayi, idan kika barii suka tafii damu muma zasu kashemu, jikin *hanna* ne yad'auki b'ari dasauri taja hannunta ta nufii Mota da ita, jaa tayi ta turje tace akwai kannena a can na b'oyesu, shiga *hanna* tace tayi itakuma ta tura wani soldier yaje ya ebosu,"
  Suka shige motocin, duk abunda akeyi MG baya ganii hankalinsa nakan wayarda akamasa ake sanar dashi mutuwar minister,"
Yana ajiye wayar *hanna* ta bud'e tashiga, shigewa jikinsa tayi ta k'ankameshi tsamm,"
  Jin yanda zuciyarta ke bugawa dasauri yanuna masa alamun ta tsorata. "
Abinda yakawo ransa kawai shine taga gawarsu minister ne a TV,"
Lallashinta yakeyi yana buga bayanta ahaka suka d'auki hanyar komawa gida. "

To be continued

Ur's
     *Z33iiyyb3rw3r*

*BIBIYATA AKEYI*

_Bismillahirrahmanirrahim_

Writing by
      © _Zaynab Bawa_
 ( _z33iiyyb3rw3r_ )

   *Allah subhanahu wata Ala yace,"  duk mutumin dakafii k'auna dashi za'a tasheka ranar tashin k'iyama, *    Ya rabb ka k'ara mana k'aunar manzonka acikin zuqatan mu, Ameen."*

    *Ka/ki kasance mai yawan tuna mutuwa, domin hakan zaisa ka/ki kasance cikin tsoron Allah."*

    *Kada ki/ka kasance mai k'askantarda mutane,"  domin bakisan wataran waye mai taimakon kaba."*

 
   *Nasiha ce*

================

  _Wannan shafii sadaukarwane ga duk wani masoyin *BIBIYATA AKEYI*  inasonku ina alfaharii daku, dabazarku nake taka rawa_💃

Page 64

*
  Najeeb ne zaune gaban mahaifinsa, jinayi mahaifinsa yana cewa Wai najeebu mai kakeson fad'amunne eyeh? "
Mai kakeson nafad'awa mahaifin yarinyar?"
 Sunkuyarda kansa yayi yace Abba wallhy bana sonta, kabani time in Sha Allah zanfito da mata. "
  Nisawa mahaifiyar sa dake kusa dasu tayi, tace tunda ya amince Kan cewa zai fito da wata, ni aganina abarshi, yanzu ai godiya zamu yiwa Allah daya amince zaiyi auren,"
  Macene za'a iya aura mata Wanda bataso tazauna Amma namiji abin zaiyi wahalan gaske."
  Maida gilashin idonsa yayi sannan yace to Allah yaza6arda mafii alkhairii,"
Bari nasamu mahaifinta namasa bayanii, zai fahimta, mutum ne mai sauk'in kai, godiya najeeb yayi sannan yatashi yafice,"
 Tunanin yakeyi aranshi yanzu idan yasamu Wanda tamasa zai sanarda mahaifinsa, dan yanzu yagama cire *hanna* ababin rayuwarsa, duk da cewa tana cikin zuciyarsa."

  Fadah suka shiga, sannan yace ma *hanna* *sweety * kishiga nizantabii, akwai aikinda zanyi."
 Kallonsa tayi tace akwai abu mai mahimmanci danakeso muyi Magana akai."
 Kallonta yayi yace kibari saina dawo, ankirani gidan minister of health yayi k'one, girgiza kai tayi tace ba k'onewa yayiba k'onawa akayi, "
  Zaro ido yayi yace,"
Kinsan me kike fad'a kuwa? "
D'aga kai tayi tace, eh nasani, yanzu hakama iyalansa sunanan na taho dasu, Kuma itace ta sanar danii haka,"
  Suna inahh? "
Yatambaya nuna masa motar bayansu tayi tace suna cikin can,"
  Fito dasu ku shiga gida inazuwa, ina zakaje? ta tambaya,"
Babu zan biyoku Abaya,"
  Zan yiwa soldier's magana ne,"
  Bud'e motar tayi tafita, sannnan ta Isa zuwaga motarsu, kar6an kabir tayi dake hannun sa'ad tafara tafiya suka biyota,"
 Side d'insu ta shiga suka biyota Abaya,"
 Kafin su zaauna har MG ya iso dan dama ahankali suke tafiya,"
   Zama sukayi, yayinda k'anannin yaran sun kasa zama zubewa sukayi ak'asa,"
  *Hanna* ce tace inkaiku kushiga kuyi wanka? "
Abida cikin muryar kuka tace wallhy bazan iyaba, yunwa nakejii,"
 Idon *hanna* har yakawo ruwa na tausayinsu, shikuwa MG binsu kawai yakeyi da kallo na tausayinsu. "
  Sa'ad ne yak'ar6e yace yau kwananmu uku bamucii komaiba."
    Alokacin Idon *hanna* hawaye yak'i tsayuwa, " Shikuwa MG sa tafin hannuwansa yayi kawai yarufe fuskarsa tausayi da takaicii, bazai barii yace komai ba. "
   Jansu d'ayan falon *hanna* tayi tad'auko wermer's d'in da sukacii abincii, zuba musu tayi kowa da nasa sannnan ta ebo ruwa da roba tabasu suka wanke hannu,"
  Faracin abincin sukayi kamar wasu mawuyacin zakii, ko k'akkautawa bbu. "
  Hassana har tana kwaruwa, kuka ne ya cufcewa *hanna* tayi saurin barin falon,"
  D'akinta tashiga ta ringa kukan tausayin bayin Allah nan, "
MG ne yashigo yaja jikinsa yana rarrashi,"
  Ce mata yayi yanzu anemo likita ya duba su, nizan tafii wajen, wani likita kake ganii za'a nemo? "
Wa kake ganii zai riqe Amana, dan ita babbarsu ta tabbatarmun, nemansu sukeyi zasu kashesu, wani likita kake ganii zai iya yin shiru da bakinsa?."
  Niasawa yayi dan MG shi kwata-kwata ma yaman ta cewa akwai doctor acikin sojojinsa."
   Shiru *hanna* tayi nad'an wani lokaci sannan tace,"
  Barina kira Yaya Jalal yazoshi,"
  Shid'in doctor ne? "
MG Yatambaya, eh kawai tace,"
  D'aukan wayrta tayi takira Yaya Jalal, ringing uku yad'auka,"
 Gaisheshi tayi Jin muryar ta kaman tayi kuka, yace, *hanna* lafiya? "
Lafiya klau Yaya Jalal, dan Allah kazo gidana, and Yaya idan zakazo kazo da first aid box d'inka,"
  Rikicewa yayi yana cewa *hanna* kifad'amun abunda yasameki? "
  Bbu da Yaya kawai saikazo dan Allah kayi saurii tana fad'in haka ta katse Wayan,"
 Tass Sanda suka tashi da abincinan,"
  Alokacin tafita tasamu wani soldier, ta aikeshi yasiyowa su sa'ad, kabir Hassana da usaina Kaya, amma su Abida da karima nata zai masu."
  D'ayan flate d'in da MG yazauna kafin auransu ta nufa dasu, dan ahad'e yake da nasu saidai wata y'ar k'ofa da corridor dake tsakanii."
  Bud'ewa sa'ad d'aki d'aya tayi, sannan ta bud'e d'aki d'aya masu karima,"
  Haka kawai ta tsincii kanta da kishin d'akin da MG yazauna tak'ii Bud'ewa,"
  Sa'ad Bayan yayi wanka yayi wa kabir, alokacin ankawo kayansu basu tayi sukasa, sannan Alokacin Yaya Jalal ya'iso, treatment d'in ciwowin dake jikinsu yayi sannnan, suka shiga danyin bacci su huta, "
  Fitowa sukayi shikuwa Yaya jalal yafi to,"
  Kallan *hanna*  yayi yace, wallhy nad'auka wani abune yafaru danaji muryarki bbu alamun walwala aciki, "  yaya ainace Maka bbu komai, Kuma kqima ksan bazan Maka k'aryaba,"
  Sallama sukayi harya juya zantafii *hanna*  tace yaya, juyowa yayi, tace kada kadamu kanka da tambayan su waye idan lokacii yayi zan sanar dakai, murmushi yayi yace, nasan baki abuu sai mai amfanii dan haka bazan damu kainaba, "
  Sallama sukayi ya wuce,  sai Alokacin *hanna* tasamu tayi sallar adhahar, dan lokacin biyu tayi," k'ara Zuwa tayi ta dubasu, har lokacin bacci sukeyi dan yaya Jalal harda maganin bacci yabasu. " sai 3 MG yadawo Alokacin *hanna* nakwance akujera ankawo abincii Amma takasa ta6awa, wata irin kewar MG dake damunta,"
  Samunta yayi ahaka yak'arasa gabanta, tana kallonsa tamiqe, sannan ta tura baki tace, takafii kawani dad'e, kinyi missing d'inane ya tambaya, girgiza kai tayi tace niii?  Aknme? "
 A'a, kokad'qn baijii dad'in amsartaba, canja akalar zancen yayi Zuwa, kincii abincii?"
  Girgiza kai tayi tace ina jiranka ne, d'an karamin tsuka yaja afili, azuciya Kuma yace kajii mun yarinya da kini bibi, natambayta tayi messing d'ina Kuma tace A'a, "
Tashi muje kicii abincin, A'a muje kafara wanka tafad'a atakaice,"
Zakimun wankan ne? "  yqtambaya, niii A'a *hanna*  tafad'a had'eda Zaro ido."
  Gyara zamansa yayi yace Kinga ni kuwa idan bazakimun ba, is better na hak'ura."
  Shareshi tayi kamar bata jisu ba,"
Ganin tana 6ata masa lokacin yasa yahaura yayi wankansa, "
 Kamshin turarensa ne doki hancinta, D'aga idanuwa tayi tana kallon sa yanda yake saukowa,"
Fara polo ce kall ajikinsa, sai bak'in wandon Jean's, sai bak'in takalmi, yatsun kafarsa sai suka haska sosai, kamar kita6a jini yafi to, gashin sai sheki farcunansa sukeyi, "
 D'auke kanta tayi kada ya kamata tana kallonsa, kawarda idanunta tayi dan karya kamata tana kallonsa, abunda batasaniba yad'ade da Ganin tana kallonshi,"
  Kallonta yayi yanda kayan yanzu sukafii k'arbanta fiyeda na d'atsu, "
  Akowani shiga tayi k'ara kyau takemasa,"
  Bayan yak'arsso sukacii abincii sannan ta d'auki basu takai musu,"
 Bayan sungama cii ne, *hanna* ta kira MG, shigowa yayi da sallama suka amsa dukansu, "
  Kallonsa dukanta suka tsayayi, dan tabbas idan Ana nufiin had'uwa MG karshe ne."
  Ran *hanna* Sanda yad'an sosu ganin irin kallon dasuke masa, "
  Kusada ita yazauna, yariqo hannunta, duka suka zauna, karimane tace sa'ad tashiga da hassana da hussaina da kabir d'aki yadawo,"
Bayan yadawo karima tafara basu labarin da mahaifinta yabasu bata rage ba Har izuwa biyosu da'akayi dakuma, ganin *hanna* datayi, tak'ara da cewa, mahaifina yanada y'an uwa dayawa, yanada dangii bila adad'in haka Kuma mahaifiyarmu ma, Amma mahaifina kune yatsaba, way'anda zasu taimaka mana, pic d'inki yabamu yace mu naimeki, dan naiman mijinki zaimana wahala,"
 Sannan tafashe da kuka, itama *hanna* kuka sukeyi,"
  Balle su abida da sa'ad da sukajii cewa mahaifinsu ya rasu, "
  Nisawa MG yayi yace, yanzu haka zannema muku wajanda zaku zauna,"
  Dan jibi sassafe zamuyi tafiya ina dawowa Akan, case d'innan zan sauka, Allah yajikansu yabaku hakurin rashinsu, dak'yar karima ta iya amsawa da amin."
  Mamaki ne yacika *hanna* ita batasan da wannan tafiya ba, Kuma tajii suu ya ambata. "
  Fita yayi *hanna*  Kuma tatsaya rarrashinsu."


  Tsawa najii andaka masa awqya, sannan akace duk yanda kasan zaka shiga kanemo su kashiga."
  Ramka ya dad'e duk wani lungu da sako munbii basanan,"
  Sannan wannan gidan, kuwa munduba bbu komai sannan akwai kayayakinsu da wayoyinsu. "
 Kuma mun dasu iya dawowa gidan, shiyasa mukasa tsaro ko dasu dawo."

To be continued

Ur's

    *Z33iiyyb3rw3r*

*BIBIYATA AKEYI*

_Bismillahirrahmanirrahim_

Writing by
      © _Zaynab Bawa_
 ( _z33iiyyb3rw3r_ )

_Like my page on Facebook :::Zaynab BAWA novels_

Followed me on instagram ::::mhiz_z33iiyyb3rw3r

   *Ka/ki zama mai biyayya Wa iyayenki/ka, domin samun rahamar ubangiji."*

 *Ka/ki zama mai tuna alkhairii duk k'an k'ancinsa."*

  *^Kada ki/ka zama mai son kanka/ki akowani lokacii," Domin manzon Allah yace imanin d'ayanku bazai cika ba harsayya sowa d'an uwansa abunda yake sowa kansa."^*

================

 _Yabon gwani yazamq dole, gakiya *SAFIYYA ABUDULLAHI HUGUMA* kinyi matuk'ar k'ok'qri, wajen fad'akarwa, awannan litttafinki na *ABADAN*,_ _Allah yasa ka miki da alkhairansa ta hanyoyi daban daban, Allah yakawo haske cikin_  _rayuwarki, kamar yanda kikasa haske muma acikinnamu_  _rayuwar,"_ _Allah ya albarkacii rayuwarki,_ _yabaki zuri'a tqgqrii,"_
_Ameen ya Allah,"_
_Ya Allah ina tawassali da sunayenka kayiwa wannan baiwa taka albarka,  kamar yanda ta tunasar damu da hadisai masu ingancii da asalii."_

   ================

Page 65

*
  Saida taga hankalinsu ya d'an kwanta sannan ta nufii nata shashin, sai 5 hameeda tazota sunyi hira sosai, hameeda sai tsokanar *hanna*  takeyi, ganin *hanna*  tak'i kulata yasata tunanin MG ya kashe bakinne, Itakuwa *hanna*  tausayin ay'annan bayin Allah ne yacika ta,"
  Dariya hameeda ta kyalkyale tace Wai, su *hanna*  anjii maza baki yayi shiru, aini band'auka akwai abunda zai kashe bakinnan ba,"
Tsaki *hanna*  taja tace da'allah malama ni kindameni, idan bazakiyi shiruba Allah saina bar miki falon,"  Dariya hameeda ta gimtse tace,"  yi hakurii bani nakar Zoman ba rataya akabanii."
 Tsaki *hanna*  tak'araja sannan ta juya mata baya. "
 Duk wata zolayqrta da hameeda takeyi bata kulata ba, dan tasan ba Hakan bane."
  Kiran sqllar magrib ne yasa hameeda tashi da niyyar tafiya, ruk'ota *hanna*  tayi tace hava Sis, gaskiya bazakitafii yanzuba, kibari yadawo sai mutafii tare,"
  Bud'e baki hameeda tayi tace, kina amaryar zaki fitafita?."
  Murgud'a baki *hanna*  tayi tace to sai me? "
  D'azuma munfita, Allah yashiryeki hameeda tace sannan tace nifa tafiya zanyii,"
  Sama *hanna*  tahaura t ebo mata turaruka kayan kwalliya, da abubuwa kala-kala."
 Har bakin k'ofa tarakota, tana shirin fita hameeda tace kinga ki koma baki tambayi mijinki ba."
 Hararanta *hanna*  tayi kawai, tad'an rakata tace beb samun abun hawafa zaimiki wuya a, Allah kinga dare yayi."
Suna tsaye saiga captain Ahmad yazo dasauri zaije masallaci,"
  Ganin *hanna*  atsaye yasashi nufan wajan, tmbyanta yayi mai sukeyi, nan tashaida masa cewa hameeda ce zata tafii, "
  Kollon hameeda yayi yad'an basar, yana gyara hannun rigarsa yace,"  tajira nayi sallah nakaita. "
Yana fad'in haka ya juya yqtafii." . Gidan suka koma Ana idarda sallah, yazo yayiwa *hanna* Magana tarakatq Har gaban mootar, sannan suka tafii tanajin kewar y'ar uwartata,"
Bata dad'e da tafiya ba labba tashigo,, da harara *hanna* tabita tace, "  wato akawoni gidanku a ajiyenii, Amma ko leqe, dama bukatarku tabiya nashigo ko?"
  Kama kinnuwanta tayi tace afuwan, wallhy tun 12 nakeso nashigo ummii tahanani Wai ba'a Zuwa gidan amare,"
  Wallhy bbu yanda banyiba tahanani yanzu ma sulalewa nayi bata sanii ba."
  Dariya *hanna* tayi tace dan Allah kaji ummii menene agidanmun da ba za'a zoba? "
  Uhmmm kawai labba tace dan batasaon taja maganar."
Hira sukayi sosai *hanna* tajii dad'iin zuwanta sosai, "
   MG nafita daga masallaci shashin ummii yawuce, zaunawa yayi akusa da ita bayan ya gaisheta ta amsa."
Cikin sakin fuska tana tambayarsa ya *hanna* sosa kayi yayi sannan yace ummii tun kafin la'asar nafita sai yanzu zan koma, fad'a ummii tabishi dashi sosai tana cewa yad'auko yar mutane zai tafii yabarta ita kad'ai,"
Hak'uri yabata sannan yasanar da ita rasuwar minister dakuma tafiyar data taso jibi,"
 Addu'a tamasa Amma Har cikin ranta bataso tafiyar ba."
 Amma dai zaka tafii da ita ko?"
  D'ago kansa yayi dakekan cinyarta, yace ummii zantafii da ita bansan lokacin da tafiyar zata d'auka ba."
Addu'a ummii tamusu sannan tarinqa masa nasiha akan yarigeta da amana. "
  D'aurawa tayi da cewa nasan kana sonta so mai tsanani Amma hakan bashi zaisa nadaina maka nasihar riqeta da amana ba."
Nasan cewa zuciya batada k'ashi, Kuma dole wataran duk dad'ii akan samuu sa6ani, k'arqmar yarinya ce, dole saikayi hakurii harda irin furucinta, sannan abuu na biyu, kaji tsoron Allah kasan yana ganinka, kada ka zalumcii yarinyar mutane."
 Nasiha sosai ummii tamasa mai ratsa jiki, "  Sannan tace yatashi yatafii yabarta ita kadai."
Tashi yayi yafita,"
Baiwuce gidaba sannin cewa tana tare dasu karima, yasa yawuce shaidawa mai martaba."
  Tashi labba tayi tace kada ummii tanemeta tamata sallama tafita,"
   Tashi tayi ta nufii shashin su karima, sanda ta tabbatar ta basu komai dazasu buk'ata sannan tajuya zata tafii, muryar karima ne takatseta, mungode Allah yasaka muku da mafificin alkhairinsa, murmushi kawai hanna tayi afili acikin ranta Kuma tace ameen, Juyawa tayi ta futa."
  Nasu shahsin tashiga, kawai ganin mutum tayi harta tsorata, sai zuciyarta ta hasko mata taga fuskan awajen diner d'insu, da fara'a tqk'arasa tana mata sannu da zuwa, daqyar ta amsa, gaisheta *hanna* tayi nan ma intisar kamar mai ciwon baki tace lpy."
Ganin haka dake *hanna* ita kanta miskilar kantane, yasa ta ebeta ta watsar."
  Sunfii 10 minute bbu Wanda yacewa wani k'ala *hanna* na danne-danne awayrta, Itakuwa tad'aura d'aya kan d'aya taunar chwengum kawai takeyi."
 K'as K'as ne ya ishi *hanna* yasa tad'anja tsaki, d'agowa intisar tayi tace, owh srry baki sanni bako, ni cousine d'in sace, owh namanta Kuma budurwarsa, gaban *hanna* ne yayi masifar fad'uwa, lokacii d' aya qirjinta yafara bugun taratara, har wani dushi-dushi take kallo,"
Srry baikamata kisani yanzu ba, Amma gani nayi bbu yanda na iya yakamta ace kinsan wata na shigowa kada ki bararraje,"
 Kinsan fa duk nisan jifa k'asa zai dawo,"
Sannan kada kiyi tunani ko wasa nake miki, ki rubuta ki ajiye Har indai inadarai, ya yareema kamar na aureshi angama."
  Ta bud'e baki zata k'arayin magana, sqiga sallamar MG, kawarda kai *hanna* tayi azuciyar tana cewa munafuki azzalumii kawai, saurin tuba tayi tana agtasfirulla tunowa da tayi cewa, ma mijinta take fad'awa way'annan kalamai koda azuciyarsane."
  Kallon *hanna* yayi yaga yanda ta kawarda kai kamar batajii shigowarsa b, Kuma yanada tabbacin tasan shigowarsa, aransane yace kowa yata6omin yar fitinar tawa, ko rshin dawowata da wurii ne yasa,"
  Zuwa dabb da ita yayi sannan yace, sweety wayo ta6ominke?"
Yitayi kamar batajishi ba danko Juyawa batayiba." Muryar intisar ce takatseshi, na cewa sannu da Zuwa ya yareema,
  Juyawa yayi ya kalleta, wata irin kunyace takamashi matarsa takasa yi masa sannu Amma wata tamasa, murmushi yayi yace yawwa habeebty yaushe kika shigo?"
Gaban *hanna* ne yayi masifar fad'uwa jinda sunan daya karata wato ya tabbata cewa, ita budurwarshi ce."
  Wani irin zafii zuciyarta tafarayi mata,"
   Kwallah yacika idanuwanta taff,"
Wannan wani irin ciin fuska ne agabanta yana kiran wata habeebty, lallai dama abunda take gudu kenan tasan cewa MG ba tsaran ta bane, dole zai nemi kyakkyawa da ajee kamarsa, "
 Shikuwa MG anasa wajen habeebty daya ambata al'adansu ne tun suna yara aka taso dasu da fad'in wannan kalmar ma y'an uwansu,"
Dan kowa yatashi dason kowa acikin zuciyarsa."
Kok'ad'an dayasan wannan kalma zata k'ona rana *hanna* dabai fad'a ba."
 Cikin kissaa da kisisina intisar tace habeeby dear inkawo maka ruwane? "
Kallon *hanna* yayi Wanda kanta ke gefe ganin ba tasan da halittarsa awajan ba sai jikinsa yayi sanyii sosai."
  K'ara cewa tayi nagaa amaryar tamu najiin kunya ne."
  Shiru yayi sannan yace ok tom, Danshi MG arayiwarsa bai iya baonsa mutumba, "
  Tashi tayi tafii hanyar falon data hango frigde aciki tanayi tana karairaya."
Shikuwa Wanda takeyi dominsa baima saniva dan hankalinsa nakan sweetynsa, tashi yayi yazo wajanta, yana tambayarta maiyafaru Amma firr tak'ii magana, bayanda beyiba hankalinsa ne yatashi, baisandai menene ba Amma ya lura kamar Zaman intisar ne ya6ata mata rai, idankuwa hakanne mai take nufii kenan?" batason yan uwansa kome? "
Dawowa tayi da robar fayrouz ahannun ta dakuma na swan, tana Zuwa ta ajiye."
  Kallonsu ahaka ya sosa mata rai amma tadake tace ya habeeby dear gashi nakawo maka, tashi yayi da toh, ya isa wajan, intisar hadda kissaa ma Amma asali tafii ki ransa da yaa yareema,ganin yanzu tanayi baya gwaleta ne yasata zak'ewa."
 Fayrouz ta Zuba masa acup yak'arba yana Sha, nanne Kuma hakurin *hanna*  yak'are ganin cewa dazasucii abinciin rana tad'auko masa fayrouz yace ta canja Amma yanzu ya k'arba, lallai yanzu tayarda namiji dakalin majina ne ka haushi ka sule,"
  Shikuwa MG ganin ita matarshine yanadakyau tasan abunda yakeso da Wanda bayaso yasa yace ta canja Itakuwa intisar da saninta da rashin sa bbu amfanii."
Tashii tayi da gudu tayi sama tana Zuwa ta kwanta akan gado tacii gaba da kuka."
 Shikuwa MG yayi niyyar binta amma intisar ta tsareshi da sururtu ba ita tasakeshiba sai 10, a lokacin *hanna* tayi kuka Har k'arfinta yak'are tayi samada 2hour's tana kuka."
  Banda nishi da ajiyar zuciya bbu abunda take iyawa."
 Bayan ya kulle k'ofa d'akinta yfara nufa, ayanayin daya ganta yai, bala'in birkitashi."
  Dasauri yak'arsa yad'agota yasata ajikinsa hannu biyu tasa tana dukansa tana tureshi, "
  Amma bai kyaleta ba, sanda ya manna ta dajikinsa yacii gaba da lallashi."
Sai kusan 10 tukun tabar dukansa tafara ajiyan zuciya, ganin yak'ii saketa yasata dallara masa cizo ak'irjii, runtse ido yayi yajii zafiin Amma zafin kukanda takeyi yafii k'onashi. "
   Ahaka Har bacci yqd'uketa, Jin saukar numfashinta ya tabatrs masa sannu hakan."
Tunanii kala-kala yarunga yi arnsa, sannan shima ahaka bacci yad'aukeshi. "

To be continued

Ur's
     *Z33iiyyb3rw3r*

*BIBIYATA AKEYI*

_Bismillahirrahmanirrahim_

Writing by
      © _Zaynab Bawa_
 ( _z33iiyyb3rw3r_ )

_Like my page on Facebook :::Zaynab BAWA novels_

Followed me on instagram ::::mhiz_z33iiyyb3rw3r

  Ka/ki zamo mai yawan karanta, ```Allahumma ajirni fi musibati, wa'aklifli khairan minha``` aduk lokacin ka/ki ke cikin wata musiba."

     Ka/ki kasance mai karanta ```Allahumma la sahla illa ma ja'altahu sahla, wa'anta taji'alul amra iza shi'itah sahla```  aduk lokacinda wani abuu yashige maki/ka duhu, kukoma kanajin wuyar aikata abun."

  *Ka/ki kasance mai karanta,* *```Allahumma antassalamuwaminkal salam tabarak ta ya zul jalalu wal'ikram```   *aduk sallah bayan ka/kin idar."*

  *Shawara ce*

================

Page 66
*
   Ahaka har kiran sallan farko."
Bud'e idanuwanta tayi ahqnkali da suka mata nauyi, har sund'an kumbura."
  Jinta ajikin mutum yasata d'agowa tana dubansa, bacci yakeyi azaune, ita kumbura tana jikinsa gabaki d'aya, tausayinsa ne yakamata tatsaya tana kallon sa yana sauke numfashi ahankalii."
  Bud'e hannunshi tayi tasauk'a da niyyar zuwa toilet tad'auro alwala dinyin sallar raka'atanil fijr."
  Har tafara tafiya ya ruqota, gabantane yahau fad'uwa dan batayi tunanin ya farkaba, abunda tamasa jiyane yadawo mata, harda cizon data masa, wata irin kunyar sace ta lullu6eta."  tashi yayi yazo dabb da ita, itakuna ta sunkuyarda kai k'asa yace ina zakije."   alwala zanyi tabashi amsa, sanyi yajii aransa, jinyadda ta amsa masa that means tadaina fushin kenan, murmushi yayi sannan yace, kiyi hak'uri kinjii, kiyi hakuri if i hurt u knwnly or u knwnly, wallhy bansan ganin hawayenki, zafii nakeji acikin raina,"
 Hawaye ya sulalo afuskarta dasaurii ta sa hannu da niyyar gogewa, yayisaurin riqe hannun yace,"
Sweety akawai abunda namiki plz kisanar dani."
Shiru tayi yajawota jikinsa, lafewa tayi ak'rjinsa, amma tayi shiru, jijjiaga yayi yace plz say ur mind dear, cikin son yin kuka tace bakai bane kace mata habeebty, gabansane yayi mugun fad'uwa, yaja hannunta suka zauna akan gado yace, Sweety duk family d'inmu haka muke kiran juna, ko bakiji haka nake kiran labba bane, turo baki *hanna* tayi tace, shine itama hadda wani cemaka habeeby dear, ita kuma labba aibabu aure atsakaninku, tafad'a hawaye na gangarowa fuskarta, babban yatsansa yasa ya goge mata hawayen, yace,"
Kiyi hakuri daga yau nabarii."
  Gyada kai tayi tace shine ka kar6i fayrouz ahannunta kasha nikuma kace nacanja maka."
   Dear ainii banga amfanin cewa ta canjaminba."
  Kinga ke matatace dole kisan abunda nakeso da wanda banso, itakuwa banga amfanin saninta ba."
  Murmushi tayi tace najii amma Allah kadena kallonta, nadena sarkin kishii, sanda yafad'ii kalmar kishii saikuma kunya takamata."
   Gyaran murya yayi sannan yace, haryanzu fa tunanin yanda za'akaisu nakeyi, suwa?" *hanna* tatambaya saikuma tace owh srry natuna way'annan yaran, sake baki MG yayi yace babbar cikinsufa tabaki samada shekara biyu amma kike kiransu yara."
 Aidai ita yarinyace tunda nayi aure itakuma batayiba."
  Bud'e baki MG yayi yace wani aure?"
Aurenta haryanzu bbu tabbacin yinsa,"
Idan kinaso asan kinyi aure kibarii nakafa miki shaida,"
Dan haryanzu baki cika farillan aurenva."
  Yi tayi kamar batajii maiyaceba, takawar da zancen da cewa." To maiyasa bazamu zauna dasuba?"
Dazamu naima musu wajen zama, cikin hikima yace tafiyace tatasomin dole ana buk'atana a russia so bansan lokacinda tafiyar zata d'aukeni ba shiyasa, cikin damuwa tace to kabarnii mana."
 Girgiza kai yayi yace bzan iyaba, banyi miki k'aryaba, jikintane yayi sanyi tace, kana ganii to mezai hana, akaisu bauchii wajan mama, nasan zata kula dasu, jijjiga kai yayi yace, kina ganin zata yarda, zanirata tace, "
  Kokuma muje kaga saimu mata sallma," harara yawulla mata yace bazakace ba, kwata - kwata kwananki ukune da barin gidan yana fad'in haka ya taashii yashige toilet."
   Dasafe kamar jiya yauma tare sukayi breakfast, bayan sungama tad'auki kulolin takai musu, tayi musu sallama sannan suka d'auki hanyar bauchii, tana futowa dakinta tanufa ta dauko  sannan ta sauko tazo dai-daishi ta zumbula hijabinta sannan tace muje."
Tashi yayi suka nufii shashin kilishi, afalo suka samii intisar na zaune, ganinsu yasa, gqban intisar fad'uwa badai harta sauko ba daga fushin datayi jiya,"
Indai hakane zatasha wahala da ita kenan tunda, tanada saurin sakkowa."
   Da harara tabi *hanna* itakuwa *hanna* tasake mata wani malalcin murmushi mai ma'ana dayawa,, k'ulewa tayi da murmushin, yasa tatashi tayi d'aki fuu, *hanna* ta d'aga murya yanda zata jita inkinahiga kikira mana umma, Tsayawa tayi cakk da bak'in ciki wai ita take aika, bata iya juyowaba tafice, shikuwa MG juyawa yayi ya kalli *hanna* yace bata girmeki bane kike aikanta?"
D'aga kafad'a yayi yace idanma tagirmeni ai yayanta nake aure, kaga dole ta girmamani, "
D'aga kai yayi yace wato kin iya kiran aurannan abaki, shigowar kilishi ne yakatse musu hirarsu, gaisheta sukayi had'eda yimata sallamar tafiyar, bataji dad'in tafiyar ba dan intisar tabata labarin yanda sukayi jiya."
Adaddafe ta musu addu'a sukuma suka fice, MG kuwa abinda ke ransa dabanne shiyasa baison sakewa yara fuska, gashi jiya d'an sakewa intisar dayayi haryau taganshi tak'ii kulashi, anyi nafarko dana k'arshe yace acikin ransa, azaune suka samii ummii gaisheta sukayi ta amsa da fara'a d'an hira suka ta6a sannan ummii tace sai zuwa jimawa zaku tafii kenan?"
Ina fa? "  yatambayi ummii, sallama da mahaifanta mana, au ummii sai munje?"
Auda haka zaka d'auki yarinya Ka tafii da ita batareda ta ga iyayenta ba."
Zuwa jimawa kubi flight kakaita sannan Idan kundawo kuje Gidan abbanta, kasan sassafe zaku wuce."
Dan haka katashi kuje kayi muku booking."
  Amsawa yayi ta to, itakuwa *hanna* farinciki yacikata, hakanne yasa tasacii kallonsa ta gefen ido, ga mamakinta taga damuwa sai taga fuskarsa asake,"
  Suna had'a ido yasake mata murmushi sannan yayiwa ummii sallama yafita."
 Tashi tayi tanufii d'akin labba, hira sukayi sosai ba ita ta, fitaba sanda yasanar da ita akan tafito sutafii."
  Basu dad'e da isa ba su karima suka isoh."
  Tayiwa baba, mama da Ammah bqyanii sun fahimceta sannan sanyi alk'awarin riqesu kamar y'ay'ansu harzuwa dawowansu."
  Dakyar *hanna* tabar gida harda d'an kukanta MG yasha aikin lallashi Bayan zuhr kad'an suka dawo, sunyi la'asar sannan suka nufii gidan umma, tayi murnar ganinsu, sosai nan da nan tashiga hidima dasu, MG kuwa yasake da ita bakamar yanda yakejin kunyar mama ba."
  Kunun aya takawo musu da zobo dayasha cocumber, yasha MG yakeyi yana santii ya kalli *hanna* ya d'aga mata zo6on yace,"  inafatan kin iya? "
Murgud'a baki tayi tace," Ko na iyama bazanyiba, auhaka kikace? "    eh tabashi amsa atakaice, ok zamu ganii, suna tashi tace, umm....  Nace dan Allah muje gidan anty afeeya mana."
  Kallonta yayi yace, idanbaki fad'ii sunana ba, ba yanda zamuje, marairaicewa tayi tace yaa yareema muje gidan anty afeeya plz."
  Murmushi yayi maikyau wanda sanda gefen kumatunsa yalotsa," yatsa tasa ta danna dai-dai kan dimpull d'in, sanda yatsanta yad'an shiga ciki, murmushi yak'arayi ya lumshe idonsa yanajin sonta cikin jikinsa."
  Sun isa gidan anty afeeya sai murna take da ganinsu tunda take da yayan nata  bai ta6a zuwa gidanba saiyau ta dalilin matarsa, dan tasan bayin kansa bane." amma tayi farinciki sosai,
  Basu dad'e ba suka tashi tafiya, leda guda tabawa *hanna* wanda nikaina bansan na menene ba."
 Har gaban motocinsu tarakosu, yaronta namusu byebye."
  Sai gidan samha, nan ma basu dad'e ba, sun d'auki hanyar gida, *hanna* tace bazamuje mugaida moddibbo bane?"
  Nishi yad'anyi kad'an yace kin tunomin ma, banje masa sallama ba, yayi murna da ganin su sosai, Addu'a yayita musu, daga k'arshe yake tambayar *hanna* inadai tana Addu'a eh ta amsa masa,"
To Allah yamiki albarka ta amsa da amin."
Sai dabb magrib suka yiyo gida, masallaci itakuma ta shiga yiwa ummii sallama saida tayi sallan magrib da isha acan sannan MG yashigo suka koma tare."
   K'arfe takwas dai-dai suna falon saiga intisar Ko sallama bbu tayi kawalliya kamar mai zuwa gasar kyau."
   Alokacin. MG nakwance acinyar *hanna*  tana wasa da gashinsa."
Ranta ya6aci ganin su haka amma tashare dan kilishi tashaida masa cewa har Indai zata ringa zuciya toh bazatacii nasara ba."
Da karai raya iso tazauna ta gaishsahi karaf *hanna*  ta amshe tace lpy klau knawarmu yagajiya?"
Takaicine yakamata lallai *hanna*  taraina ta itance zata gaidata." Murmushin dole tayi ganin idon MG abud'e, can *hanna* tace plz habeebty dan d'aukomin ruwa afridge, kinjii tafad'a tana dariyar shu'umancii."
  Intisar Yi tayi kamar batajii ba, kawai tsinkayan muryan MG tayi yana cewa, kihad'omin da fresh milk, bayadda ta iya haka tatashi tanufii fridge fresh milk kawai tadauko da cup takawo, masa ganin bbu ruwan yasa yace ina ruwan yake? "
Mikomin kikoma kidauko mata, bak'in ciki ne yacikata, dazata miqa masa sanda tad'an rusuna saman boobs d'inta yafito." mistakely idon MG yakai wajan rintsa idanuwansa kawai yayi atake tsikar jikinsa yazuba."
   Rintse idanuwansa yayi *hanna* ta cafke gorar tace plz d'aukomin ishirwa nakejii."
  Sanda ta galla mata harara sannan ta nufii fridge tad'auko ta dangwara mata."
 Aranta tace ohowdai kind'auko."
Tana zaunawa baifii da 5minute ba *hanna* tace dan wanke mun plate dinda mukaacii abincii, guda biyu ne bbu yawa, bak'in ciki kamar yakasheta hararar datakeyiwa *hanna* kuwa kamar idanuwanta su fad'o." kenan 2 minute bata kulava, yace bakiji mai tace miki bane?"
Tana k'unk'uni tatashi tad'auraye, ita arayuwarta ba wanke wanke takeyiba."
Tana gamawa tafito tasamu *hanna* itakad'ai MG yashiga d'aki."
  Kallon *hanna* tayi tace bani kikayiwa wulakancii ba? "
Hmm ayanzu bazaki gane matsayinki ba harsai nashigo gidan tana fad'in haka tajuya tafice."
  Kulle k'ofa *hanna* tayi, tahaura stairs d'akinta taje tayi wanka tafito sa wata y'ar ficiciyan sleeping dress tayi."
  Sannan tayi light off  ta kwanta, tasan bbu amfanin rufe k'ofan dan yanada key d'in."
 Cikin bacci taji kamar ana kiranta, Bud'e ido tayi sannan ta kunna bedside lamp, MG ne tsaye idanuwansa sun canja kala kamar maijin bacci."
  Zama yayi kusa da ita sannan yajawota jikinsa, tana shirin yin magana yahad'e bakinsu waje d'aya."
Taso hanashi amma hakan yafaskara,"  shin yana mata wasu abubuwa masu wuyar fad'a yasata fara tureshi,"
Yakai hannuwansa cikin rigarta tayi saurin riqe hannun tana kuka, ganin kukanta ya tsananta yasashi saketa yana bata hakuri."
  Ahaka bacci yad'auketa."
  Da asuba sanda MG yayi wanka kafinnan yayi sallah itakuma tayi sallah, sannan suka wuce aminu kano airport, K'arfe bakwai jirginsu yad'aga zuwa airport."

To be continued

Ur's
     *Z33iiyyb3rw3r*

*BIBIYATA AKEYI*

_Bismillahirrahmanirrahim_

Writing by
      © _Zaynab Bawa_
 ( _z33iiyyb3rw3r_ )

_Like my page on Facebook :::Zaynab BAWA novels_

Followed me on instagram ::::mhiz_z33iiyyb3rw3r

   *Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agareshi yace, duk wanda yayi sallah yaban ya idar ya karanta Ayatul kursiyu, bayan kowacce sallah, bazai mutu cikin wannan dareba face Allah yagafarta masa duk zunubansa."*

    *Manzon Allah zira da amincin Allah sutabbata agareshi yace, duk wanda yakaranta suratul iklas sau koma arana, bazai gushe ba harsai angina masa gida acikin aljanna."*

   ===============

    Page 67

Jirginsu yasauk'a lokacin K'arfe shida 6:00.pm dai-dai a agogon rusia." tun kafin suyi landing motocii sunzo tar6ansu, yanda kasan za'ayi bak'on shugaban k'asa, dan k'asar sunaji dashi sosai, su suka reneshi, sukasan mahimmancinsa,
  Wani k'aton estate taga motoccin sun danna kansu ciki, soldier's ne tako ina, kana ganii kasan sun iso yanda mazaje(soldier's) suke zagaya ko'iina sukeyi ta gun's ahannunsu, a'inda taga sunnufa, wani babba daga cikin estate d'in, abakin gidan motocin suka tsaya, Bud'e musu k'ofa akayi, inda yana fitowa suka k'ame, zagayawa yayi ya kamo hannun *hanna* har zuwa bakin gidan, itadai *hanna* takasa magana amma zata iya cewa Ko a pic bata ganii ba, amma gajiya yahanata tsayawa ta kalla, wani soldier ne dake tsaye abakin k'ofan yasa wani card a k'ofan bud'ewa tayi sannan MG yaja hannun *hanna* suka shiga, sun gajii liqis, d'akin su dake k'asa suka sauka dan hawa saman aikine."
    Suna shiga *hanna* tazube akan bed, da kallo MG yabita, baitsayaba yawuce toilet yayi wanka had'eda d'auro alwala, fitowarsa yasamu *hanna* harda fara bacci, suka da ita yamaytsa yasa hannu yawatsa mata sauran ruwan dake jikin gashin kansa."
  Firgigit tatashi tana mutsuttsuka ido, tana ganin MG taturo baki ita adole tana bacci yatsheta." Tashi ki shiga wanka, yafad'a, nida kabari natashi tukunna *hanna* tace,"  zaro ido yayi yace kinsan sallolinda ke kanki kuwa?"
  Tashi kiyi wanka muyi sallah nima baccin zanyi."
   Tashi tayi idanuwanta yasauk'a akan packs d'in da ke cikin sa, aranta tana fad'in komai n MG unique ne, Ko a wrestler's d footbooller's bata ta6a ganin pack's kamar nashi ba, yanda kasan anjerasu, kowanne d'aya nabin d'aya."  ganin ta tsaya tana kallon packs d'insa yayi murmushi mai kyau wanda sanda kumatunsa suka lotsa, aransa yace yarinya zaki shigo hannu ma."  afili kuma yace kina kallon yanda kikayi biting d'ina Ko?" lakatan hancinta yayi yace aibakya jin magana."
Rud'ewa tayi tafara k'ame k'ame, dan tasan yagane batabon take kallo ba."   magana take shirinyi yasa yatsunsa biyu yarufe bakin yace shiiiishhh, tashi kishiga wanka, tashi tayi tanufii toilet  tana k'unkuni, tana cewa, sai ya wani fitowa damutane d'aki dgashi sai towel, Ko kunya batajii, sarai yajita amma yashare, yacigaba da zura jallabiyansa." Ta dad'e tana wanka sannan ta saka hannunta zata ciro kayanta dake jikin switch, garin janyo kayan ta kunna shower, aikuwa shaaraff yajike kayan."
   Takaicii ne yacikata ganin duk kayan sunjike sai towel, danma towel d'in nada d'an girma, tafii 30 minute, kafin ta iya fitowa, tana tafiya tanajan gefen towel d'in sannan ta dukun kune gaban towel d'in."
 Lokacin data fito MG harya idar da sallolinsa, yana zaune abakin gado."
Kallo yake K'are mata, yanda yaga lamps d'inta awaje yasashi tsintar kansa cikin wani yanayii."
  Tashi yayi yafara nufota, ganin haka tafara jahh da baya, shima biyota yakeyi, tajuya da niyar gudu kawai yacafkota, girgiza kai tafayi, yajawota yahad'ata da jikinsa, babban yatsansa yasa yanna zagaye lips d'inta yace, wa kika cewa marar kunya?"
Shiru tayi magana, matse lips d'inta yayi da yatsunsa biyu, sanda tad'nyi k'ara yace badake nakeyi ba?"
  Nan ma shiru bbu magana idanuwanta sunyi zuru-zuru, yace ok bari ingwada miki k'arshen rashin kunya, yana fad'in haka yasa hannu yafara kok'arin kunce towel d'in."
  Xaro ido tayi tana girgiza kai sai Alokacin tasamu bakin magana tace dan Allah kayi hakurii, wallhy bazan sake ba, zaki sake yace aibakyajin magana, Allah kuwa bazan sake ba."
  Brushing lips dinsa yayi akan nata yace kima sake, sannan ya saketa, yace kije kiyi sallah, sanda tarama duk wani sallolin dake kanta, ta yi addu'oii tace wai mutuminnan meyake nufiine?"
Badai d'aki daya zanzauna dashi ba."
   Ya lumshe idanuwansa yayi pillow da hannayensa, taje kansa tatsaya, jin mutum akansa yasashi bud'e ido, yace uhmmm, inane d'akina?"   tace dashi, murmushi yayi yace kibarii gobe inza6a mana, amma yanzu bacci nakeji, nikuma yunwa nakeji tafad'ii,"
  Tashi yayi yad'auko snacks da drinks yajonata dashi, harta fara cii, tajuya takalleshi tace kai bakajin yunwa ne?"
Injii yabata amsa takaice, to meyasa bazakacii abincinba."bacci nakejii saina tashii, ammm,,,,, yakatse da shiiiii gamacii kizo mu kwanta bansan surutu, iya yanda zata iya tacii, sannan tabar sauran tazo tashige bargo dake garin da sanyi, bacci sukayi sosai Basu suka farkaba sai cikin dare, nanma sallane tatadasu na isa dan basuyita ba."
  Matsa masa tayi sanda yacii abincii, dan dama tun sunkusa esowa aka tanda musu abincii kala-kala, Ka d'an yataba, sannan itama yasata tacii , da asubama agida MG yayi sallah tareda *hanna* sanda sukayi azkhar da karatun qur'ani, sannan suka koma bacci,"
  Sai wajen 8 suka tashi, suka samu anshirya musu breakfast, abaki tabashi kamar kullum shima yabata sannan sukayi wanka suka shirya."
 MG baibar anbar kowa yafara shigowaba acewarshi, baihutaba tu kunna."
  Daukan wayanshi yayi yaga misscall dayawa, da ummii su labba, amma na intisar yafii yawa, d'aya bayan d'aya yafara kiransu, yana shaida musu isowar su."
  Daga k'arshe yakira intisarr, yafad'a mata ya iso yaga misscall d'inta yagode, da tad'ii taso rikeshi amma, yanuna mata yagajii dayawa bai hutq ba, sallama tamasa, sannan yakatse wayar."
  Kallon *hanna* dake gefensa yayi yaga hankalinta baya kansa yasauke ajiyar zuciya."
   Daki yanufa yashirya cikin kakin sojojinda yayi matuk'ar kar6ansa, yafito Kallo, tabbishi dashi tace ina zakaaje?"
Office dear am srry, bazan dad'e ba zandawo kinjii, nayiwa shahid magana zaituro matarsa, dai-dai ita yazo yamata peck agoshi, sannan yad'an zugunna dai-dai lips d'inta yamata light kiss, yace bye take care dear."
 Batace komaiba haryazo bakin k'ofa ya tsinkayo muryarta tana cewa, Allah yakareka, tsayawa yayi cakk wani sanyi ya ziyarceshi hak'ika yajii dad'ii wannan addu'a, murmushi yamata sannan yafice." Su karima kwana biyu kawai sukayi da mama wata irin shakuwa ta shiga tsakaninsu, jinta sukeyi kamar mahaifiyarsu."
Kula kuwa suna samu dai-dai gwargwadoo."
   Haka Ammah ma nakula dasu, sai baba shima yana iya bakin, k'ok'arinsa, sosai yaran suke bashi tausayi."
 

Su senator bbu irin neman dabasuyi ba amma bbu su bbu labarinsu, komai ya canja."
Dan sun tabbata akwai shedu masu k'arfii agun yaran."

  Itakuwa hafsat da c_bilal soyayya tayi k'arfii, yanzu haka yadameta akan yanaso yasamu iyayensa, itakuma tabshi dama, ya shaida mata wannan tafiyar ta sukayi zai wuce, dake shii d'an libya ne."
  Dama tun bikin yadameta akan yanaso yaje gaida iyeyenta, ta shaida musu cewa sai angama, da aka gama yace kwana 3 kenan amma taki amincewa ganin haka yasata bashi dama kawai."
   Itakuwa *hanna* da zaman kad'aicii yadameta, tad'auki wayanta tayi ta kiran y'an gidansu daganan takoma kan su ummii."
  Sai can matar shashin tashigo, sanda sukasha hira sai kusan 3 MG yadawo."

To be continued

Ur's

     Z33iiyyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*

_Bismillahirrahmanirrahim_

Writing by
      © _Zaynab Bawa_
 ( _z33iiyyb3rw3r_ )

_Like my page on Facebook :::Zaynab BAWA novels_

Followed me on instagram ::::mhiz_z33iiyyb3rw3r

     *Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agareshi yace, ku koyarda yaranku alqur'anii, dominshi lallai mai karanta qul'anii, yace (fii zillillahi) yana cikin inuwar Allah, yauma da (zilla illa zillahu) yace ranarda bbu wata inuwa sai inuwar Allah, wato ranar qiyama, Allah kabamu ikon karanta alqur'anii, ameen ya Allah*

   *Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agareshi yace, ku ringa tuba zuwaga Allah, wato karinga karanta astagfirullah wa'atubu ilaik, kana qaskantarda kanka zuwa gareshi, koda sau d'ari arana d'aya."*

================

Page 68

*
  Sai kusan 3:00pm kafin MG yadawo gida, ganin dawowarsa yasa matar shahid yimusu sallama ta fita, k'arasawa yayi wajan *hanna* data turo baki kamar zai ta6o k'ofa, dariya yayi ya Girgiza, kai yace yar rigimata anfara kenan,  k'arasawa yayi tajuyar dakai gefe, yana murmushi yatar6o fuskanta yace, beb yane turo baki tak'arayi, yace ko yunwa kikeji?"
Kamar zatayi kuka tace bakai bane, nine nayi meh?"
Katafii kace zaka dawo dawurii kuma kak'ii dawowa,"
Owhh srry dear kinsan nikaina bansan zansamu aikii hakaba, amma ai duk laipynki ne, laipyna kuma?"
Eh laipynki ne mana tunda naje Nigeria kikak'ii ki barnii harsanda na auroki tukunna, kinsan cewa 6 month kenan banzo k'asarnanba?"  nazo nasamu matsala dayawwa, yanzu dole sainayi making dinsu up,"
  Dan haka yanzu kinga ai ba laipyna bane."
  Sake fuska tayi tace tom muje kacii abincii, ke kincii ne?"
yatambayeta  A'a banciiba inajirankane, ok tom muje kimin wanka sai incii abincii."
  Tabb mujedai kayi wanka, kafin ka yi sai inhad'a mana abincinn,"
Girgiza kai yayi yace wataran basaina roqa bama."
  Ta6e baki tayi tace ai watarana kace."
  Haka yashiga wanka tafito masa da kayanda zaisa, ta ahjiye akan bed, tafita tashirya musu abincii."
     Fitowa yayi da armless shirt dakuma 3quater, k'arasowa yayi dining d'in , yanacewa beb baki tausayina kikabanii wannan kayan, ana sanyii fahh."
 Tabace komaiba haryazo yazauna, zuba abincin tayi aplate d'aya kuma d'an kad'an, kallonta yayi yace ya kika zuba kad'an?"
 Ni bazanciba tabashi amsa atakaice, bazakiciba kuma?"
 Eh tace,"
Meyasa to?"
Nifa banta6a cin irin wannan abincinba."
 Kallon abincin yayi sai alokacin yatuno cewa itafa bata saba cin wannan abincin ba,"
 Tashi taga yayi, tace kazauna kacii mana, A'a yabata amsa atakaice tace to meyasa, bazan iyacinn wani abuu sweetyna bataciiba, je kid'auko mayafinki mufita na nema miki abincii, toh tace sannan takoma, shikuma yashiga yad'auko fanko na jallabiya sabuwa yabud'e yasaka, itama tafito suka fice,"
Had'eda sojojinsa, wanda bai ebii dayawaba kawai ya ebii wanda zasu rakashine, dan bbu halii yatafii shikad'ai."
Ahanya sai zuba masa labarii takeyii yayi shiru, daga alamu akwai abunda yake tunani."
  Har suka iso bakn wani k'aton mall wanda zaiyi mata shopping na mak'ulashe."
  Har *hanna* tabd'e k'ofa zata fita yariqo hannunta yace, kijiranii mana sarkin y'an saurrr,,,,,, aibaki k'arsaba yajii k'aran harbii wanda da'alamu harbin wajensu ake hara."
  Lokacii d'aya kuma aka bud'ewa motocin wuta sosai, tako ina harbii akeyi har yakaiga anharbii, daywa daga cikin sojojinsa."
  Shikuma *hanna* kawai yake tunani yariqe kanta yakwantar k'asa, itakuwa *hanna* 6arii kawai jikinta yakeyii, sai kuka takeyi tabi tad'agawa MG hankali, yarasa yanda zaiyii, yanaso yafita amma ta duk'unk'uneshi."
Dakyar yasamu yab'anbare yace ta rufe idanuwanta, ta kuma toahe kunnanta kada ta bud'e saitajiishii, d'aga masa kai tayi, yace yaewa rufe, dank'e idanuwan ta tayi sjlhikuma yabud'e tad'ayan gefen zai fita, dan dama duk soldier's dinsa sunfita saurashi kad'ai, jin karara bud'e kofa yasata bud'e idanuwa tace, inazakaje?"
Plz karka futa zasu kasheka,murmushi yayi kawai yace, ilove u yasakai yafice, yarufo mata k'ofar, garam, itakuwa dake motar bullet proof ne yasata k'in kwanta, sai juye juye takeyii, neman MG kawai takeyi, can ta hango lokacinda c.Ahmad ya cillo masa bindiga, MG yamatuk'ar harzuqa ganin yanda wasu dage cikin sojojinsa akwance, ga mutanen garii yanda abun yarutsa dasuu, ta wajan  da mutanen suke kawai MG yanufa, harbi kawai yakeyii, duk wanda yaharba baya harbinsa awajenda zai tashii, kisa kawai yakeyi nana danan hankalin *hanna* yatashi ganin yanda MG ke kisa ko alamun imanii bbu, wata irin tsanarsace ta d'arsu aranta, Kukan yak'ii zuwa mata gabaki d'aya, aikuwa sai numfashinta yafara sama-sama, acikin motar ta sulale ta sumee ko numfashii bbu."
   Su kuwa MG yad'auki 30minute kafin yagama clearing komai, mutum d'qya suka barii araye, a''inda zasu bincikeshi dansusan wajen zamansu,"
   Alokacin aka fara d'bar wanda suka samu raunuka, suka yi asibiti dashi, acikin sojoji, bbu wanda yarsu. Saidai munanan raunuka, su kuwa sauran mutane yaro d'ya dakuma wani mutum sunmutu,
 Yana bud'e kofa yaga *hanna* ahaka, dasaurii yasa hannu ya d'aukota, bayadda beyiba amma *hanna* ko motsii,  ambulance yanufa yasata duk hanklinsa atashe, ko numfashi batayi yad'aurata akan bed d'in nan likitocii suka shiga vata taimako kafin a''isa asibiti."
  Hannunsa yaduba ynada yabacii da jini, tsorone yakamashi,  badai anharbeta nan danan MG yafara surutai kamar wanda yazauce, yanayii yana, hucii, idanuwansa sunkad'a sunyii jajirr, kamar jinii ganin dagske jinin daga jikinta yake,
 Sun d'auki 20 kafin suka is hospital, dama tuntunii ansan da zuwansu, ana isa suka karbi *hanna* suka shiga bata taimakoo."

To be contineud

Ur's
     Z33yyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*

_Bismillahirrahmanirrahim_

Writing by
      © _Zaynab Bawa_
 ( _z33iiyyb3rw3r_ )

_Like my page on Facebook :::Zaynab BAWA novels_

Followed me on instagram ::::mhiz_z33iiyyb3rw3r

 

  *Manzon Allah tsira da amincin Allah Su tabbata agareshi yace, har indai kakaranta wannan addu'ar da safe."* ```Allah humma innii as'alukal jannah, wama yuk'arribunii ilaiha min qaulin wa amal, wa a'uzubika minal narr, wama yuk'arribunii ilaiha min qaulin wa amal."```
*Bazakq gushe kana karanta wannan addu'ar ba, face Aljannah tayi addu'a tace, ya Allah ina roko ka kawo wannan Bawa naka cikina, wuta sai tayi addu'a tace Allah ka kare wannan Bawa naka daga shiga cikina."*

   *Akwai wani lokacii da wani mutum yazo wajan Manzon Allah yace ya rasulillahi, inaso kabanii shawara, sai Manzon Allah yace masa  *(la tagdabb)*   *kada kayii fushii, sai wannan mutumi yak'ara cewa ya habibullah inaso kabanii shawara,   thumma k'ala rasulillahi *(lah tagdabb)* *kada kayii fushii, sanda sukayi haka har sau uku da Manzon Allah."*
 *Manzon Allah (SWA) yace ku nemi tsarii daga fushii tahanyar karanata a''zuubillahi minal shaid'anurra jimm."*
  *Allah karabamu da yinn fushii dakuma yanke hukuncii cikin fushii."  Ameen ya Allah."*

================

Page 69

*
  Likitocii Basu dad'e akanta ba suka fito, suna fitowa wajen MG suka nufa. Babban liktanne yace, Major ka kwantar da hankalinka, she's out off risk now, but tana buk'atar rest, for about 2hour's danta razana."
  Haryanzu hankalinshi ba akwance yakeba."
Tunaninsa jinin dayaganii ajikinta nameye. riqe hannun doctor yayi yace jininda take zubarwafa?"   badai harbinta akayi ba?."
 Girgiza kai liktan yayi yace, tsoratan datayii ne yasa, mensturation d'inta yazo, a wannan lokacin, dake date d'in yakusa yasa jinin ya matso kusa, kuma dalilin tsorata datayii yasashi tsinkewa, amma bayan haka bbu komai, sai alokacin MG yafitar d numfashi yana furta Alhmdllhy kawai dan bbu abinda zai iya cewa."
   D'akinda take yawuce, yana bud'e k'ofar da sassafar yak'arasa bakin gadon, yariqe hannunta, itakuma tana baccinta, numfashinta nasauka ahankalii."
Fuskanta yayi fayau, bakinsa yakai kan goshinta ya sumbata, yak'ureta da ido kawai."
  Wayrshice tayi k'ara, dube - dube yafara danshi baiyi tunanin cewa wayarsa na aljihunsa ba."
  Jin k'arar ajikinsa yasa yakai hannunsa aljihu, yana ta6awa kuwa yajita cirowa yayi, nan ake gayamasa meeting nanda 3hour,"
  Kallon *hanna*  yayi duk saiyajii bbu dad'ii, kasan cewaar dole yatafii kan lokacin yacika, hakan yana nufiin bazata tashii agabansa ba kenan."
Wani d'an siririn tsaki yaja wanda saida yafito fili duk saiyajii ransa ya6acii dan baiso ace yarabu da *hanna*  kona secound d'aya balle tanacikin wannan halin."
Yakusan 1hour ahaka Jin kiran sallan magrib ya tuno ko la'asar baiyiba."
  Tashii yayi ya shiga toilet,yad'auro alwala, dake da sabon carfet ashimfid'e sai yayi sallan la'asar akai sannan yagabatar da magrib."
  Dake soldirer's d'insama asibitin daa akawosu kenan yasashi fita yadubasu kowanne, wasu harsun farfad'o, wasu kuma haryanzu bbu alamun farfad'owa."yana komawa d'akin da *hanna*   take shida wasu sojojin da aka turo masa daga baya, had'uwa sukayi da abid dake zuwa shida matarsa da d'ansu d'aya."
  Ganin matar abid yasa shi, tafiya amma dakyar dan hankalinsa yanakan *hanna*  shida abid suka juya suka tafii, Su uku suka had'a motocinsu da sojojin Su zuwa wajan meeting d'in."
  Sun d'auki awowi dayawa wajan meeting d'in, awajanne ake shaida musu cewa yanda aka  musu da cewa nan da 1month akeso sukawo
 k'arshen wannan terrorism d'in, d'an Sun kashe sojojin dayawa da musu mulki, a wannan karan suka kawowa MG harii wanda k'asahen dayawa bazasu iya taasashiba, gwara, Su fataucesu tun kafin dawowarsu."
  Ahaka Ahaka aka tashii a meeting d'in." Alokacin *hanna* tayi kusan  2hour's datashi, ganin tafarfad'o bbu MG awajan wani bak'in ciki yakamata wato bazai iyajiranta tafarka ba kenan?"
 Zai tafii damuwarsa."
  Suna barin wajan bbu yanda basuyi da MG ba ko gida yayi ya, gani yakeyi kamar yayi shekara baiga *hanna* ba yasan aduk yanda take yanzu tafarka." da d'an saurinsa ya shiga cikin asibitin ko soldirer's d'insama bai jiraba."
Yana bud'e k'ofa, idanuuwan sune suka had'u waje d'aya wani irin haushinsa ne yakamata."
   Hawaye tajii yana k'okarin zuwa Mata tayi saurin kauda kanta."
  Dasaurii yak'arasa yayi hugging nata tight har wani d'an nishii tayi,ganin matar abid awajen kawai sai kunya takamata, saketa yayi yanaso ya hango kwayar idanuwanta amma firr taqii dantayi k'asa da kanta."
  Hannunta yake murzawa alokacin yana tambauarta tacii abincii tace, d'aga kai kawai tayii, dan idan zatqyi magana to kukane Zai biyo baya."
 Sai  Lokacin MG yalura da matar abid dake wajan, cewa yayi au namanta abid yana jiranki yana waje."
   Dariya tayi tace yaushe zaka tuna, aina lura idankana tareda matarka baka ganin kowa."
  Shiryawa tayi, sannan tajuya zata yiwa *hanna* sallama narai-narai tayi da idanuwanta tace dan Allah karki tafii, mukwana anan."
  A'adai gashinan yadawo nasan cewa tun d'azu dakikak'ii magana shii kike jira."
  Tana fad'iin haka tajuya tafice, *hanna* Tana ganin tafita tajuyar dakai hawaye nabinn fuskarta, kwanciya tayi tajuya bayanta, yazo dabb da ita yana Mata magana amma tak'ii kulashii, duk yanda yaso tamasa magana amma tak'ii, ahaka har tayi bacci."
  Sai kusan 2:00.am kafin tatashi, nan ma firr tak'ii ta mishi magana, Koda yamatsa sai tasa masa kuka."
  Zuwa yayi da niyyar yariqeta ya rarrsheta, tace ni karka ta6anii, wallhy nadad'e banga marar imanii irinkaba."
  Har zaka iya kashe raii wallhy saidai, kamaidanii gidanmuu."
  Runtse ido yayi dan yasan haka zata faruu."
  Bayadda za'ace taga mijinta yayi kisa kuma ta aminta dashi awawannan lokacin, gashi yanada tabbacin ko kokuwa mai k'arfii *hanna* bataa ta6a kallo ba."
  Ahaka yak'arasa tana kuka amma ya manna ta ajikinsa."
 Ba yadda batayi takwace ba amma kuma abun ya faskara,"
Kwantarda kanta tayi tacii gaba da kuka, furzarda iska mai tsafii kawai yakeyi, dan baison kukanta, zafii yakejii acikin zuciyarsa, kokad'an baison 6acin ranta."
MG ayanda yad'auki abun ba haka yayi zato ba."
Dan har akayi sallah bai runtsa ba *hanna* rikicii kawai takeyii."
 Duk yanda yaso yayi calming d'inta abun yak'ii haka ad'akin yayi sallah, daga ita harshi tun breakfast najiyane a cikinsu."
  Sai a d'akin yatashi yayi sallah Zuwa safiya dole yanemii sallama wajan likita dan bazai iya da rikicin *hanna*  a asibiti ba."
   Zuwa 9 aka sallamesu, amota ko kulashii batayiba shikuma duk wani motsin ta yanakan idanuwansa." Suna isa yace ta shiga tayi wanka, bbu musu tashiga tayi dan itama kanta  wani irii takejin jikinta."  tana fitowa awanka taahirya, saiga matan abid da Mata shahid sunshigo, abincii suka kawo Mata tacii sai ita, MG ganin tacii abincin hankalinsa yakwanta."
    Sai alokacin shima yasamu yashiga wanka, yad'ansa wani abu abaknsa."
  Labarin abunda yafaruu harya karad'e duniya, yanzu haka ma, Su ummii sai neman layinsa sukeyi."
  Saida yayi wanka sannan yakunna phn dinsa wayan ummii ne tafara shigowa, d'auka yayi daga yanda ummii Ke magana kasan hankalinta atashe yake."
  Kwantar Mata da hankalii yayi yace Mata bbu abunda yasameshi, dakyar ya lallasheta yad'an Kwantar Mata da hankali."
  Haka ma mai martaba kowa idan yakira saiya tambayi *hanna* dan bbu wanda yayi zaton tana wajan abun yafaruu, kowa yabarii akan tana gida, shikuwa ganin haka yasa baifad'a musu ba dan baiso hanakalinsu yatshii."
  Intisar data kirashi kuka takeyi tsakanii da Allah dakyar yasamu tayi shiru."
Ajiyar zuciya kawai takeyi, yanzu yarinyar nabawa MG matuk'ar tausayii, dan yasan tana sonsa sosai, shikuwa kosaau d'aya bai ta6ajin sonta bayaga na y'an uwantakaba, duk lokacinda akace wani abuu yasameshi, takanfii kowa nuna tashinn hankalinta."
Yana tausayin duk wani mai kok'arin shiga yanda *hanna* take, yasan ko takalmin *hanna* saiya fishii soyuwa a'iidanuwansa, Koda kullun *hanna* zata ringa yanka neman jikinsa shidai yanasonta, akullum yanajin zafii idan yaga 6acin ranta."
  Shikansa yasan wannan jarabawace ta ubangijii, ance zuciya nasan mai kyautata Mata, amma shi nashi zuciyar har indai akan *hanna* ne ko munana Mata takeyii yanasonta."
 Nisawa yayi ya lumshe ido, afili yafurta insonki *hanna* har iya k'arshen rayuwata."
  Tashii yayi yanifii falo dan sake ganinta, Koda bata d'ago ta kalleshi ba yakanjii dad'ii aransa, yakanjii sanyii."
  Juyawa yaje zaiyi wayanshi tad'auki k'ara,"
   D'agowa *hanna* tayi tadubeshi sannan takawar dakai, tad'anja siririn tsaki, kallonta matar abid tayi tace wani wajanne Ke miki ciwo?"
 Girgiza Mata Kai tayi kawai ta kwanta, ganin ta lumshe ido yatsaya daga nesa yana k'are Mata kallo."
Wani dad''ii ne yaziyarcii xuciyarsa ganin yanda dangin *hanna* suka damu dashi tun d'azu suke kiransa dan sujii lafiyarsa, duk abinda yashafii *hanna* yana mutuntashi yana bashi kimarsa."


Komawa d'aki yayi yabarsu sunata hira, kiran sallah ne yafito dashi, masallaci yawuce, bayan yadawo baicii komai ba Saida ya tabbatar da cewa *hanna* tacii abincii."

  Kwana biyu MG duk yabii yarame yakuma lalace dan ko kollon yanda yake *hanna* batayi."
  Har zazza6i sanda yayi."
  Gashi saura 5day's Su tafii war wanda mutuwa ko rayuwa, bbu wanda zaitafii kuma yayi tunanin cewa zaidawo."
  Duk wanda yatafii wannan yanada tabbacin cewa dawowarsa mai wahala, yariga da yasadakar,"
  Acikin y'an way'annan kwanakin duk yanda yaso shawo kanta abun yafaskara,"
   Ana washegari zasu tafii MG yazo d'aki yasamu *hanna* takoma sama danta dad'e da canja musu d'aki." Da sallama yashiga, aciki ta amsa, ya nemi kusada ita yazauna kusada ita tashi zatayi yasa hannu yamayarda ita, kawarda kanta gefe tayi."
  Yasa hannu yadawo da kanta yace *hanna* plz kiyafenii, gobe da k'arfe 12:00am zamu tafii *hanna* bbu tabbacin dawwarmu, *hanna* kiyafeni, kitaimakmin kada na mutu baki yafemunba."
  Kitaimaka naga farin cikinki Koda sau d'aya ne."
 *Hanna* zaitafii da kunchii araina kasancewar nabarki cikin bak'in ciki."
  Kukane ya kufcewa  *hanna* rugumeta yayi ajikinsa yana rarrashinta Haka kawai *hanna* ta tsincii kanta dajinn zafin tafiyarda MG zaiiyii, jitakeyi kamar tabishi,  amma takasa nuna masa hakan."
  Ahaka suka wayii garii bbu wanda yarintsa yanajin sanyii jinta ajikin sa."
  Dasafe dakyar suka karya itadai bata sakee masaba bakuma tanuna tana fushi dashiba tana tsaka tsakiya,
Amma cikin zuciyarta tanajii zafiiin wannan tafiya so sai."
  Dakyar suka iya breakfast bbu mai walwala acikinsu."
  Shi MG damuwarsa yaga tasake amma hakan yagagara."
  Ahaka har lokacin tafiyarsu tazo ta,  wasu daga cikin sojojin harsun fara tafiya."
  Ba'adade ba aka bukacii fitowar MG, idon hanna ne yaciko damm, kawarda fuskanta tayi kada yaga hawayen amma abun yafaskara sanda yaganii."
Jawota jikinsa yayi yace plz kada kiyi kuka kada kisa natafii jikina bbu kwarii."
  Ytasansa yasa yashre Mata hawaye amma abun sai ahankali wasu nabin bayan wasu."
  Had'e bakinsu yayi waje d'aya yafara kissing d'inta, sumd'auki samada 20 minute ahaka, duk yanda MG yayi *hanna* bata hanashi ba, Dakyar yasaketa, yana maida numfashii, kasa had'a ido dashi *hanna* tayi tayarda ita yayi suka nufii hanyar fita, yazo dabb da k'ofa *hanna* tadamke hannunsa yajuyo tafara Girgiza masakai damuwarsa yajii maganarta amma abun yafaskara, rabonda yajii muryarta tun kafin tayi rashin lpy."
Duk yanda yaso tayi magana tak'ii, kawai sai tasake hannunsa takoma dagudu."
   Ahaka yajuya yatafii."
  Yau *hanna* Kwanan Su MG biyu da tafiya, amma ko waya bbu dakira wayarsa kuma akashe,
  Iya tashin hankali *hanna* ta shiga gabaki d'aya tadawo marainiya ta rame, tana kewar MG sosai, yau tatashi dason Jin kashin MG, kayansa ta bud'e tanabii d'aya bayan d'aya tana shanshanawa tana lumshe ido, wani diary ne yafad'o mai kyan gaske, daga alamu Labarin MG ne aciki."
    Tsintar kanta tayi da son karantawa, b'alle botill na jiki tayi sannan ta zuge zip d'in littafin, pics d'intane ya bayyyana acover na buk drin gabantane yafad'ii, tasandai wannan pic d'in yayi kimanin 10yrs bud'e shafin farko tayi. "

_Kumin afuwa gobe ba lallai kujini ba, amma idannasamu dama zqku jini._

To be continue

Ur's
     Z33iiyyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*

_Bismillahirrahmanirrahim_

Writing by
      © _Zaynab Bawa_
 ( _z33iiyyb3rw3r_ )

_Like my page on Facebook :::Zaynab BAWA novels_

Followed me on instagram ::::mhiz_z33iiyyb3rw3r

    *Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agareshi yace," kuyawaita yimun salatii ranar juma'at."*
*Kamar yanda gobe da kasance babban rana juma'at, Allah kabamu ikon yiwa manzonka salatii, ya hayyu ya qayyum ya ziljalalu wal ikram."*

   *Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agareshi yace, ku ladab tarda y'ay'anku, da abubuwa guda uku."*
*Yace ku koya musu son Annabinku, sannan ku ladabtar dasu da son mutanen gidan Manzon Allah."  Abu na uku shine ku ladabtar dasu da karatun alqur'anii."*

================

 _Ina kike aminiyar kwarai qawar albarka, kisani ina sonki ina alfahaari dake_  _*murjanatu(gimbiya)*   wannan shafin nakine ke kad'ai."_

================

   Page 70

Page na farko taga anrubuta."   I LOVE HER."   abunda aka rubuta kenen, na biyu kuma SHE'S AN ANGEL."
 sake bud'e third Page d'in tayi, SHE'S STUBBORN,  abunda aka rubuta kenen."
Murmushi mai kyau *hanna* tayi sannan ta bud'e fourth Page d'in, SHE WAS BORN IN 29/MARCH/1998."
Page na biyar tada bud'e ne taga rubutu mai yawa zama tayi sosai sannan ta fara karantawa Kamar haka."
   On 29/march/2007."  the day I first saw her."
Runtse ido *hanna* tayi, sannan tacigabada karatu."
  Da misalin k'arfe 7:45.am." na safiyar litinin, tushen aiki."  alokacin kowani d'alibi k'ok'arinsa yaga ya isa makarnta."
  Takowani lungu ka leqa dalibaine Da uniform kala-kala."
  New GRA sky crest d'alibaine birjik gaban makarnta assemly akeyi kowane d'alibi tsab-tsab dake kasancewar ranar farkon satii."
  Brown d'in skirt ne dakuma milk shirt sannan sai brown mini hijab."
  Yawancin student d'in kayanda ke jikinsu kenen."
 Sai kuma gefe d'aya dana ganii Brown skirt Da milk d'in hijab Da riga."   Alamu yanuna cewa  junior ne masu wannan shiga."
  Daga can gefe kuma yarane Da green d'in check, bayan angama assemly d'in kowanne yanufii class d'insa."
  Motocii ne suketa wucewa hanyar."
  Wasu Motocii ne sukazo ajere da'amu akwai mai mulkii cikintq."  Motocii guda biyarne duka hud'u nagaba Da baya an musu paint na sojojii, yayinda d'aya Daga cikinsu takansace bak'a wuliik."  yarane makill, wanda suke jira su tsallaka, uniform d'insu ya ban tanta dana d'yqn skull d'in. Tsallaka titin sukesonyi, amma yawan motociin dasuke wucewa yahansu, tsaye suke cirko-cirko, MG ne dake cikin dake cikin bak'in motar yayiwa guard d'insa magana aka su kashe titin student su tsallaka."  tsayuwar motar ne yasa student suka fara tsallakawa, hanakalin MG ne yakai kan wata mota, stliet ce ta tsaya bakin sky crest ta sauke Wata yarinya, Da bazata wuce shekara tara ba."
   Sannan motar ta juya zuwaga makarantar dake opposite d'inta sa'adu zungur."
  Sauke sauran yaran yayi, wanda da'almu y'an uwan tane,  amma abun yabashi mamaki ganin ita ansauke ta a private schooll sukuma y'an uwanta ansauk'esu a government schooll."
  Juyawa yayi zauwaga yarinyar dayaga ansuke."
  Gabansane yafad'ii da ganin yarinyar yarasa dalili kawai yakasa d'aga idanuwansa daga kanta."
K'ura mata ido yayi tsam, magana takeyi wanda baijin mai take fad'a, amma kuma daga alamu yagane cewa magana ake mata akan sandal datasa, kowani student yawuce sandal na kafansu brown ne kokuma black."
 Ita kuma nata pink ne."
  Bayadda ba'ayi tacire sandal d'inba amma tak'ii, dariya abun yabashi ganin yanda yarinyar keda taurin kai."
  Ahaka har kusan 15 minute sukuma soldier's d'in ganin haryanzu baiabsu order natafiya ba, yasa kowa yayi shiru."
   Gateman d'in ganin tak'ii cirewa ne yasa su cewa tom sai anmata bulala na latti, turjewa tafarayi tana kuka amma haka bbu imani, sanda ya zuga mata d'aya runtse idanuwa MG yayi danhar ajikinsa yajii zafin bulala."
  Bud'e idanuwa yayi yaga yanda take ihu."
  Ganin tana kuka yasa Gateman d'in yace ta wuce, tafiya takeyi tana kuka hankalin MG inyayi dubu yatshi ganin yanda tatafii tana kuka."
   Ahaka yatsaya harta shige."
 Juyawa yayi ya kalli driver ya nuna masa wani d'an waje anrubuta kobii senima asaman wajen duka sukayi parking."
  Yunwa sukeji duka dan saukarsu kenan zasu wuce zaranda hotel, su huta k'arfe biyu sunada meeting."
   Sai 1 aka tashi su *hanna*  sunfito y'an primary kad'ai."
  MG leqe yakeyi amma baiganotaba Sai can wata yarinya tanata kwala kira *hanna* *hanna*  direction d'inda take kallo ya kalla dan sunan yamasa sosai, idauwansa yayi tozali da yarinyar dayagani d'azu."
  K'arasawo tayi tace wai nii menene kiketa kirana?"
  Bud'e baki MG yayi ganin k'aramar yarinya amma Sai shegen tsiwa."
   Yarinyar ce tafara magana tace d'azu anty tace muyi wshing d'inki is ur birthday today."
  Eh kawai *hanna* tace sannan takawarda kai tanufii wajan wani mai rake dake bakin titii, sayan raken tayi sannan ta koma ta zauna, bata dad'e dad'e zamaba wasu frnd d'inta sukazo, tsayawa sukayi cirko-cirko akanta, hqrara ta aika musu sannan tace menene kuma zaku wani tsayamun aka,,,,,,,, aibata k'rasaba suka juye mata bokitin ruwa." Razana MG yayi ganin yanda tasa ihuu da kuma yanda numfashinta ke sama-sama."
  Had'e baki sukayi sunacewa Happy birthday, saurin fitowa MG yayi daniyar taimakonta, alokacin motar babansu ta danno wajan tsayawa yayi cakk, ganin babanta yafito dasaurii ya nufeta babbar riagarsa yacire yanad'eta yad'auketa zuwa mota."
  Ganin su MG yatsayayi yarasa dalilin dayasa Yarinyar tatsaya masa araii, baibai wajanba har saida ya ga yafiyansu."
  Juyawa yayi ya kalli captain bilal dake kusa dashi yace."
  Wancan mai raken kaje kabashi jaree, banso yak'ara sayarda rake."
  Dahaka suka isa masaukinsu, sannan suka wuce meeting."
  Washe gari yakamata MG yakoma amma haka yakoma washegarii da safe."
  Dai-dai lokacinda *hanna* tazo jiya."
  Sanda yaga shigarta har zuwa tashinta sannan ya koma."
  Alokacin *hanna* hawaye kawai take gogewa, ko batazo k'arshe ba tasan MG masoyintane."
  Share hawayen tayi tacigaba da karatuu."
   Sanda yayi kwana uku yana zuwa makaranta yana jiran tashinta."
  Ana hud'unne yabita har gida."
  Tun daga lokacinda yaga gidansu yabar captain bala da captain bilal masu jiranta."
  Koda yaushe suna k'ofar gidan idan anguwa zata tafii itqda yayyaunta to suna biye dasu."
  Ko shago *hanna* taje ta siya abu tom wannan mai shagon Sai anbashi jareenda zai iyayin uku ko hud'un nasa nad'a."
  Mutane daywa sun samu sauk'i daga talaucii ta dalilin *hanna*  wanda ita kanta batasan anyi ba, shikuma wanda yakeyin shima baisanii ba."
  Koda gyada *hanna* taganii ahanya tasaya mai gyadanan Sai anbii har gidan iyayenta anmata kyauta."
  Alokacin da MG yake wannan abun shikansa baisan mai yake ji gameda *hanna* ba."
 Aranar juma'a *hanna* ta zo makaranta bbu P.E dress, abakin gate aka tsareta, MG na cikin mota dan dama yadad'e awajan."
  Duk yanda akayi da *hanna* qkan tasa tace ita bazata sakaba."
 Kamar yanda ya lura da *hanna* kullum Sai anyii rikici da ita akan pink d'in abuu."
  Ahaka bayanda suka iya suka barta dan idanda saboo yakamata su saba da halin *hanna*."
   Washe garii MG yakoma kano."
  Bayan yaje bai b'oyewa mahaifiyarsa abunda yake faruwa dashiba duk da dai bai shaida mata cewa wacece Yarinyar ba?"
  Kuma bai fad'a mata shekrunta ba."
Alokacin ummii ta shaida masa cewa sonta yakeyi."
  Bbu yanda batayi akan yafad'a mata gidansu da adress d'insu ba."
  Amma firr yak'ii yace mata dasauran lokaci."

   Zuwa sunday Sanda yakoma bauchii dan kwana biyu dayayi baiganta ba jiyakeyi Kamar ya shekara duk yavii ya susuce."
   Yana isa mai makarntarsu yafara nqima yashaida masa komai kan yanaso acanja uniform zuwa pink, mai makarantar ganin kud'ii nan danan ya amince."
  Monday dake student kowa yazo za'a bashi unifor kyauta."
  Pink colour *hanna* tayi murna sosai."
A''inda iyayen yara sukayi mamakin ganin yanda mai makarntar yakeda son kud'ii amma harya iya kyautan uniform."
  Ahaka *hanna* tacigaba da karantawa har zuwa lokacinda suka shiga secoundry na dariya tayi dariya na kuka ma tayishi."
 Kukantane ya tsananta Alokacin da taga MG yarubuta sojojina sun dawo masu saida rake dan ta dalilinki, sojojina sun zamq masu shago ta dalilinki."
  Sojojina sun zama y'an taxi ta dalilinki."
Duk wani taxi takika shiga iya tsayon girmanki, ina tsare dake, wannan abuun nayi shine dan kar ki had'u da wanda zai sayemun zuciyarki."
 *Hanna* sojojina har kwasan kwata na layinku sunyi dan tsaron lafiyarki."
  Aduk yanda kike sojojina *BIBIYARKI SUKEYI*."
  Aduk lokacinda da kike wani abuu idan kin cire mutanen gidanku tom ina *BIBIYE DAKE* k'arfin da kukan *hanna* yayinee yasata barin karatun Sanda tayi kukanta t koshi sannan kuma afili ta furta tabbas banyii laifii ba danace *BIBIYATA AKEYI*   Share hawayenta tayi sannan tacigaba da karatun."

   To be continued

Ur's
     z33iiyyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*

_Bismillahirrahmanirrahim_

Writing by
      © _Zaynab Bawa_
 ( _z33iiyyb3rw3r_ )

_Like my page on Facebook :::Zaynab BAWA novels_

Followed me on instagram ::::mhiz_z33iiyyb3rw3r

   *Manzon Allah tsirada amincin Allah su tabbata agareshi yace."  Duk wanda yakaranta wannan addu'a, la'ila ha illallahu wahdahu la sharika lahu, lahul hamdu wa lahul mulku yuhyi ayumitu ahuwa hayyul layamutu wahuwa ala kulli shai'in k'adir."  Allah zai rubuta masa lada dubu sau dubu sannan zai yaye masa zunubi dubu sau dubu."*

    *Yanada kyau karanta addu'ar nan bayan tashi daga bacci."   Alhmdllhillazii ahyana ba'ada ma amatana wa'ilaihinnushur."*

================

Page 71

 *
 Share hawayen fuskarta tayi sannan tacigaba da karatun."
  Page na gaba da bud'e, Alokacin da tafara girma, alokacinne fargaba yadad'u wa MG yanda yaga dare haka yake ganin rana haka yake kallon dare, Koda bacci yakeyi mafarkinsa bai wuce na *hanna* ba, akwai lokacinda wani malamin su yadaketa akan batayi note ba sanadiyar korarasa daga aikii kenan."
   Tsayawa *hanna* tayi da karatun tarufe bakinta da hannunta tabbas tasan lokacinda wannan abun yafaru kuma tundaga wannan lokacii bbu wanda yak'ara dukanta tabbas abun har mamaki yake bata, tarasa dalili sai yanzu tasamu dalili."
   Cigaba tayi da karatun, quarter na teacher's dinku sojojinane, narasa wani irin so nakeyiwa *hanna*  ko alabarii banta6ajin Labarin makaman ciyar soyayaya irin wanda nake mataba."
  Ko a film banta6a ganiiba balle azahiri."
  Hak'ika wannan jarabawa ta ubangiji ne, wanda ke jarabtar bayinsa Aduk yanda yaso kuma Aduk lokacinda yayi niyya."
   Hak'ika wannan jarabawa ta fad'a kan MG, duk lokacin birthday d'in ta, Aduk k'asarda MG yake saiya dawo yayi wshng d'inta birthday ya ajiye mata gift da Hannunsa, har yakawo lokacinda *hanna* tafara mensturation, ana farko harsanda suka dangana da asibiti, ganin bayan ansallametane sukayi baincike abunda yakwantarda ita, aikawa MG details na komai sukayii."
   Awatan yasa aka canjawa likitan asibiti zuwa wani babban hospital, sannan yad'auko wata female doctor wanda takware afannin mata, yasata a asibitin, wani month da *hanna* suka dawo bayan tagama yimata treatment saita buk'aci data runga zuwa tun kafin date yacika."
  Ahakanne yad'an samu relief, shikuma   MG yananan yana bibiyar rayuwarta, Ahaka abubuwa sukayita tafiya dan har zuwa gama schooll ne secoundry,"
  Tayi jamb ta samu admissn, tun daga ranarda tafara zuwa makaranta tun wannnan rana MG ke cikin fargaba, dan yasan yanayin jami'a dole za'asamu wanda zaija hankalinta."
  Yanda yaci sa'a *hanna* bata kasance d'aya daga cikin masu rawar kan samarii ba."
  Kodan batada farin jikinsu ne ohow🤷‍♀, Yad'aura da cewa, nasha wahala sosai na rashin yin aure da wuri sannan na fuskanci matsaloli da dama tafuskan hakan."  Amma har indai akan jiran *hanna* ne zan iya komai zan iya jira ko hakan yana nufiin zan iya had'uwa da wata matsalar, banjin arayuwa, banda ta fannin iyaye akwai wani abunda yafimun ita mahimmancii aduniya, banjin ko rayuwarda nakeyi takaimun tata,"
  Bansan maiyasaba amma nasandai haka kawai nayanke shawarar barinki harsaikinkai 19 kafin naasanar dake, Sai gashi, zuciya ta tana taraddadin hakan, Kuma amma nakasa sanardake ko mahaifanki."
 Akowani lokacii nakan rasa wani abune ke tsayarda nii daga yin hakan."
  Sau dayawa naso sanarda mahaifina amma kuma konaje gabansa ban iyace komai, Hakanne yasa na tattara lamurana na miqasu ga Allah."
  Ina addu'a kawai dannasan Allah zaijii kaina tun dashi yad'auramun wannan lalurar kuma zai yayr mun."
   Wani page ta bud'e dasabon rubutu kamar haka,    Ayau na kasance cikin bak'in ciki, marar misaltuwa shine ranarda d'aya daga cikin soldier's d'ina yasanar dani cewa, *hanna* tafito daga lecture's har taje siyan abun shago, yabige wani mutum taje fad'uwa har  yakamata, aranar nashiga rud'ani dan hankalina yakasa kwanciya,  nakasa yarda da wannan mutum, K'arfe tara dai-dai na dare, tracer na wayar *hanna* ta  nunamin kan call yashigo wayarta."
  Ya tsincii kansa da son Jin wayan, bud'e wa yayi ya fara jii, kafin yagama duk yabii yashiga tashin hankali."
  Suna gama wayar akayi tracing na wayar sa."
   Alokacin yasamu duk wani impormation dayakeso akan sa."
Ya nemo kuma yasanii, amma bai yi Tunaniin zai iya rabashi da *hanna* ba, dan alamu masu yawa sun nuna tana sonsa."
   Ahaka MG yacigaba da rayuwar k'uncii amma hakan baisa yakaraya ko Sau d'aya daga sonta da kuma burin auranta ba."
    Shidai kawai yabata lokacii ne itada saurayin nata."dan kokad'an jikinsa bai bashi cewa wancan zai aurii *hanna*  ba, yana yawan yin mafarkai akan cewa ya aurii *hanna*  dayarnsu, Koda mafarkai ba gaskiya bane amma kuma yanajin dad'ii da wannan mafarki."
  Ranarda labarii yazomin cewa *hanna*  sun rabu da najeeb, narasa awani halii na tsincii kaina, ina tsananin tausayin *hanna*. "
   Bayan karanta page dadama ne, yabud'e page d'in da MG ke cewa."
      Yau ne takasance ranar farin ciki agareni, *hanna*  ta yarda zata aureni, Koda nasan batasona amma inada yak'inin wataran zata sonii."
  Labarai ta runga karantawa kala-kala duk randa suka had'u da MG ko Murmushi tayi sayya rubuta."
  Balle yakaiga dariya."
  Har zuwa ranar d'aurin aure su, har diner da aka yi sanda ya rubuta."
   Har zuwa tafiyarsa."
  Rufe littafin tayi tana kuka sosai wanda har zuciyarta zafii take mata, tana cewa Allah natuba, natuba Allah wayyo Allah na, mijina kayafeni, wallhy nima inasonka, Allah wani irin soyayya ta ka jarabcii wannan Bawa naka da ita wanda komai nayi baya ganin laifiina."
   Allah natuba, tanayii tana riqe cikinta, dan zuciyarta tana mata suya gabaki d'aya haushin kanta takejii."
  Ga wani irin son MG dayaa kamata wanda ita kanta batasan akwaishi tun daba, ko kuma lokacin yashiga ba."
  Tafii 30 minute Ahaka amma kuma bbu sauk'i zazza6ine ma yafara rufeta." Tashi tayi ta niyar gyara akwatin, tana d'agashi yafad'o yazube, pics d'intane ne acike da k'atuwar trolly d'in tun tana yarinya har izuwa girmanta, abundai bbu yadda za'a fassarashi."
   Bata k'ara kaiwa awaa d'aya ba zazza6ine mai zafii yarufeta, ko iya d'aga hannunta batayi, Ahaka matar abid tashigo tasameta, kiran doctor tayi amma shima soldier ne, yaduba ta yakawo mata maganganuwa, batafii kwana 2 ba zazza6in yasauka zai kuma azabar sonjin muryar MG takeyi tanasonjin awani halii yake ciki?."   takira wayarsa hatta gashi baya shiga gashi 2 weeks kenan bbu wanda yajii Labarin su."
  Itakam *hanna*  Idan kaganta tayi rama sosai, kullum ararrashinta matan abokansa sukeyi, dakyar takecin abincii."

   Ummii ne zaune tasa afeeya agaba, fad'a takeyi kawai akan itadai aje ad'auko mata y'arta bazata iya da rashin abu biyu ba bbu yareema kuma bbu matarsa *hanna* dan kimanin 5day's kenan kota kira wayar *hanna*  ba'a d'agawa."
  Duk yanda sukayi su shawo kan ummii abun yagagara."
  Suma kansu Suna cikin tashin hankali.".     Awashe garii afeeya tashirya da tatafii rushia da niyar dauko *hanna*."

   To be continued

Ur's
     Z33iiyyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*

_Bismillahirrahmanirrahim_

Writing by
      © _Zaynab Bawa_
 ( _z33iiyyb3rw3r_ )

_Like my page on Facebook :::Zaynab BAWA novels_

Followed me on instagram ::::mhiz_z33iiyyb3rw3r

    *Manzon Allah tsirada amincin Allah su tabbata agareshi yace, (Hajaral muslimu akhahu.") wato musulmi ta k'aurace d'an uwansa."  Manzon Allah SAW, yace (kasafki damihi) wato kamar yazubarda jinin jikinsa ne. Hak'ik'a mai yanke zumunta yana cikin tashin hankali, Allah ka k'ara mana son y'an uwanmu acikin zuk'atanmu."   Ameen ya Allah."*

 

   *Manzon Allah SAW yace, ita wannan duniya da kuke ganii, (alsijnil muminun) wato takasance kurkuku wajen mumini."   Yayinda tazama aljannah wa kafirii."   Ya Allah ina rok'onka kada kasa dad'in duniya ya rud'emu, mukasa aiwatar da abunda zai fisshemu aranar alqiyama, Ya rabb, kabamu ikon bauta maka akowani hali muka tsincii kanmu, sannan Aduk abunda muka mallaka muyi amfanii dashi wajan bautata maka."  Ameen ya rabbil izzatt."*

================

  Page 72

*
   K'arfe had'u na yamma jirginsu afeeya yasauk'a arussia, taxii tatsara ya kaita har zuwa estate na manyan sojoji."
   Tun daga farkon layin sojojina azube, ako ina, shiga wajan yayiwa afeeya matuk'ar wahala dakyar suka barta tashiga izuwa estate d'in."
   Koda ta isa bakin gate d'in bbu yanda batayiba anhanata shiga dan wajen manyan sojojine, acikin sojoinma sai kanada appointment kake shiga, ko kuma yakasance kana d'aya daga cikin masu tsaron wajen."
  Har magrib afeeya na wajen, takira wayan *hanna* ba'a picking." har ranta ya6aci sosai  dan tayi kusan 3hour's tana kira."
   Wani tunani tayi nan danan hankalinta yatashi, batasan Kowani abune yafaru da *hanna*  ba yasa bata picking."
  Gashi Duk wani shaida dazai nuna cewa ita y'ar uwar MG ne batazo dashiba balle tasamu tadubata ko lpy, dan tasan hakan ba halin *hanna* bane."
   Itakuwa *hanna* nacan ko breakfast batayiba dake yau cikin matan abid da shahid bbu wanda yaahigo."
 Dakyar tasamu tashiga tayi wanka dan yunwa tacii jikinta sosai."  Koda bayan tafito wayarta tad'auka taci gaba d kiran MG kamar kullum."
Abinda tasabaji shi akace wayar akashe take,"
Kukane ya kufcemata batasan awani hali MG ke ciki ba, ta tabbata da yana lpy zai nemeta, maiyasa zaimata haka?" maiyasa sai lokacin da take matuk'ar sonsa zai tafii ya barta."
  Dakyar ta tsagaita kukan ganin magrib tana neman wucewa, ta tashi jirii ne yafara ebarta, dasauri tazauna."
Sallarma sai azaune tayita."
   Bayan *hanna* ta idarda sallan   tana kan pray mat, tana kuka tana yiwa mijinta addu'a, dan tasan a halin yanzu abunda yafii buk'ata kenan."
  wayarta dake can gefe ne ta k'arayin ring dan dama tadad'e tanajii tak'asa picking."
 Cikin kasala tatashi amma yanzu jirin ba sosai ba tanufii phone d'in, dushi dushi take ganin wayar, picking tayi sannan takara a kunnenta, afeeya ne tasauk'e ajiyan zuciya Jin anyii picking."
  Tana d'agawa bata jira amsa sallama ko gaiasiwa ba tace *hanna* ina gate, sunk'i su barnii nashiga."
  To kawai *hanna* tace ta ajiye wayan." dakyar tafuta ad'akin zuwa falo nanma sanda tazauna tahuta tukunna, ta isa zuwa bakin k'ofa, d'aya daga cikin soldier's din dake tsaronta taaika dan bazata iya futaba."
  Tana fad'a masa aikar tazube awajen ta kwanta tana numfashii sama-sama."
   Shikuwa yana zuwa baisamu matsala wajen shigoda itaba."
  Sanda yabud'e mata k'ofa yana riqe da trollyn d'inta sannan tashiga."
  Adab k'ofa taga *hanna* kwance cikin saurii taqarasa ta riqota tana cewa, *hanna* *hanna*  tanajii ana kiranta tayi k'okarin bud'e idanuwanta amma tana bud'e wa saiya koma luuu yarufe, dan wani irin jiri takeji wanda ko idanuwanta bazata iya bud'ewa ba."
 Riqe ta afeeya tayi, Jin tana numfashi sama-sama yasata fita ariikice tayiwa soldier's magana nan danan akayi asibiti da ita." Asibitin dake cikin estate d'in suka wuce da ita, ana zuwa doctor yafara dubata, bai dad'e ba akayi admitiing d'insu."
   Afeeya duk atunaninta ciki *hanna* kedashi, Allah Allah takeyi likita yazo  ya tabbatar mata takira ummii tafad'a mata, dan tasan hakan zai kwantar da hankalin ta."
  Bayan doctor yashigo, afeeya tace doctor meyake damunta?"
Nisawa yayi sannan yace batacin abincii ulcer takamata har tayi chronic  sannan tanqsaka damuwa sosai hakan har yana shirin sanya mata hawan jini."
   Afeeya bata iya cewa komai ba gabaki d'aya tqusayin *hanna* ne yakamata tasan damuwarta bazai wuce akan mijinta ba."
  Doctor ganin hankalinta baya jikinta yanakan *hanna* yasa yayi gyran murya."
  Tana juyowa yace karki damu nan da safiya za'ayi discharging naku."
Daxaran drip d'in sun k'are zata farka."
Idan tatashi asamamata wani abunda zataci."
  Y'ar karamar drawer yanuna mata yace,"  Duk wani abunda zaku buk'ata yana cikin nan."
 Sannan yace bayan tacii abincii Idan tatashi tashige office na nurse akwai injections da madicines da zatayi taking."
  Godiya afeeya tamasa yafita sannan kuma ta k'urawa *hanna* ido tana Mamakin irin ramar da tayi."
 K'arfe 10:00 drip na *hanna* yak'are."
Sai, 10:25pm kafin ta farfad'o, waige waige tafara yi dan sanin inane yanda take."
  Ganin afeeya tayi dake kan sallaya tana sallah batasan farkawarta ba."
  Shiru *hanna* tayi tak'ura mata idanuwa har ta idar tajuyo da niyyar duba *hanna* ganin idanuwanta abud'e yasa afeeya tataso dasaurii ta isa wajen ta, sannu tafara yi mata itakuma banda Murmushi bbu abunda takeyi."
Tea tahad'a mata tabata dakyar tasha."
Sannan tad'anji k'arfii."  Juyawa tayi ta kalli afeeya tace Anty afeeya zanyi sallah."  d'agata tayi ta taimaka mata zuwa toilet tayi alwala."   Sannan kuma tafito azaune tayi sallah."  Tana sallah afeeya tafita taje takira nurse, dakyar akayiwa *hanna* allura sanda tahad'a da kuka."   har sanda tasaka Anty afeeya dariya. "  wajen shan maganii kuma ba'asha wahala sosai ba." riqeta afeeya tayi ta kwanta ajikinta tacii gaba da kuka."  dakyar tasamu ta sakata tayi bacci."
 K'arfe 7:00am akayi discharging nasu."

  _Kuyi hakuri da wannan wallhy Yau sai ahankali."_

To be continued

Ur's
      Z33iiyyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*

_Bismillahirrahmanirrahim_

Writing by
      © _Zaynab Bawa_
 ( _z33iiyyb3rw3r_ )

_Like my page on Facebook :::Zaynab BAWA novels_

Followed me on instagram ::::mhiz_z33iiyyb3rw3r



   *Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agareshi yace, kalmomi masu k'arfii akan harshe."* ```thaqilatan fil mizan```  *way'anda suka kasance masu nauyi akan mizani."  kuma habibtan fir rahman."  way'anda suka kasance mafii soyuwa awajan, Allah subhanahu wata alah."  sune SUBHANNALLAHI WABI HAMDIHI, SUBHANALLAHIL AZIM."*

    *wani mutumi yasamu Manzon Allah SAW ya tambayashi."  yace* ```ya rasulillah man haqqan masu bihusnii sahabatihi````
*Waye ya wajaba akan mutane sufii kyautatawa."*
 *Sai Manzon Allah yace mahaifiyarka, Sai wannan mutumii yak'ara cewa Sai kuma wa?"  Sai Manzon Allah yak'ara cewa mahaifiyarka, Sai wannan mutumii yak'ara cewa thumma man, fa qala rasulillah thumma ummuk."   sannan Sai Manzon Allah yace thumma abuk."  yanada kyau ka kayautatawa mahaifiiya dan sanda Allah ya ambaceta sau uku kafin ya ambacii mahaifii."  Allah kabamu ikon kyautatawa mahaifanmu."*

================

   Page 73

*
 Gida suka nufa, suna shiga afeeya tataimakawa *hanna* ta shiga wanka itakuma tafita dan shirya musu breakfast."
 *Hanna* bata d'auki lokacii wajen wankan ba tafito dan ba k'arfiin jikinta takejii sosai ba."   abakin bed ta zauna ta had'a kai da gwuiwa hawaye na zubo mata, tunaninta d'aya awani hali MG yake ciki."   sallama afeeya rayi aqofar d'akin jin ba'a amsaba yasata shiga dan atunaninta bata futo awanka ba."   ganin *hanna* tayi tahad'e kai da gwuiwa alamun kuka takeyi, dasaurii tak'arasa wajenta, ta ta6a kafad'unta *hanna* tayi saurin d'agowa cikin muryar damuwa afeeya tace *hanna* wai meke damunki ne?  Kinsan kuwa mai doctor yace?  Plz kidena saka tunani acikin ranki, jin haka yasa *hanna* fashewa da kuka tace anty ya zanyii wallhy wayarsa bata shiga tunda yatafii ko sau d'aya bamuyi waya ba kuma haryanzu bbu wanda yasan halinda suke ciki, k'ara wani kukan take tana anty nashiga uku wallhy idan wani abu yasameshi bazan iya rayuwa bbu shiba, anty kitaimakenii yadawo."  wallhy inasaonsa anty duk abunda nafad'a k'aryane ban ta6a k'in saba, tasaka hannu akayi tana cewa nashiga ukuna."  idon afeeya tabb yacika da kwalla tausayin *hanna* dakuma tausayin kansu narashin sanin halinda d'an uwansu yake ciki yakamata, tabbas tasan aranda akace sun rasa MG tashin hankali yashigesu har iya k'arshen rayuwarsu, mutumne wanda yafii  kowa soyuwa aran dangii."   bawai dan kud'insa ko mulkinsa ba a'a saidan kawai Allah yayishi dashiga ran alummah." zama tayi abakin gadon ta rungume   *hanna* tana tana bubbuga bayanta dan duk wani abunda zaifito abakinta yanzu kuka ne shiyasata yin shiru kawai."   hwaye tabb a'iidonta."
   D'iga hawayen idonta yafarayi abayaan *hanna* aikuwa  *hanna* ta k'ank'ameta tsam taqara sake wani kukan." shafa bayanta kawai afeeya takeyi dan bbu wata kalma dazatayi amfani da ita wajen nusarda ita, tasan dolene hanna ta damu, tausayinta ne ya dad'a malale zuciyar afeeyah,
  Sunfii 15 minute ahaka  sannan afeeya  tasaka hannuwanta tashare hawayen idonta sannan ta d'ago *hanna* dake jikinta  tasaka hannuwanta tana share hawayen tana mata murmushi cikin sigar lallashi tace kiyi shiru abunki kinji? jiya muna asibiti najii wasu soldier's suna cewa next week zasu dawo, dan haka ki kwantarda hankalinki cikin, nan danan *hanna* tafara murmushi, cikin zumudi tafara murmushi hawaye nazuba mata tace, da gaske?"  jijjjga kai afeeya tayi tana gaskanta mata zancen tace kwarai kuwa."
  Nana kaga fiskan *hanna* yahad'e hawaye dakuma  murmushi riqo hannunta  afeeya tayi tace maza tashi muje mucii abincii, *hanna* tace anty nak'oshi 6atarqi anty tayi tace hanna kina nufi idanya ganki ahaka zaiji d'ad'ine?"  gara kicii abincii zuwa nanda satinn kya murmure sai yayi farin cikin ganinki, tashi muje tariqo hannunta, sai alokacin hanna tuna batada kaya ajikinta daga  ita sai towel kunya ta kamata ta sunna kai  ganinhaka afeeya ta gane mai take nufi, tasaketa tace kishirya saiki sameni afalo, sanna tamiqe tafuta, Tana gama shiri tafita falo tasamu anty afeeya tagama had'a musu komai zama tayi suka faracin abincin, batacii dayawaba  tatashi da duk da damuwarta tad'an ragu amma fa haryanzu bawai dadin abincin takejii ba."
   Tashi tayi takoma kan kujera tazauna ta lumshe ido ita ba bacci takeyiba amma kuma hankalinta ba'a wajen yake ba, zuciyarta  duk wani abunda yahad'a ta da MG yakeyi,  abubuwane yashiga yi mata yawo acikin kwakwalwarta,  na murmushi tayi murmushi, duk abunda takeyianty afeeya na kallonta, itama murmushin tayi tana girgirza kai, tarasa wani irin so sukeyiwa junansu." wanda d'ayabazai iya rayuwa bbu d'aya ba."
   Wucewa anty tayi dan gabaatarda sallar walha, tabar *hanna*  sai juye juye takeyi amma idanuwanta alumshe."  wani farin ciki ne acikin zuciyarta Jin  cewa MG yakusa  dawowa."  koba komai yanzu hankalinta xai kwanta, zata samu peace of mind."
 

================

   Hava mama yanzu dan Allah 1month hadda 2weeks kuma kice bazan fita ba."  dama su saleem d'in basu fita yawo bane dasai suje, dan Allah mama karkice a'a wallhy nagaji dazaman gida."  nisawa mama tayi tace toh karima tsoro nakejo gani nakeyi kamar idan kika futa wani abuu zai biyo baya."  wallhy bbu komai mama bbu wani abunda zai biyo baya."   yanzu zan sayo miki nadawo."  nisawa mama tayi sanna tace ok tom kishiga wuntii dan tafii kusa, sai ki dawo dawuri."
  Abida dake kusa dasu tace mama aike kika kulata, sai kace dole ance mata  karta fita amma sai taurin kai."   harara karima ta galla mata tace banson rainii ansa dakene?  Kawarda kai gefe abida  tayi sannan karima tacigaba dacewa dan Allah mama wallhy yau haka kawai nakeda sha'awan fita, nisawa mama tayi sanna tace kid'auki kud'in amma kada ki dad'e."   toh tace sannan ta shiga ta zumbulo hijabii, tafito duk da haka hankalin mama bai kwanta taba tace, karima dawo kisa niqab bbu musu tadwo tasaka sanna tafice."
   Tana fita da wuce wuntii market, tayi sayyayanta tsab, sanna tad'auki hanyar dawowa,  round about dake wuntii tana tsayae tana jiran keke napep, alokacin motan najeeb ya danno kai, ya juya  titi kawai idanuwansa suka sauka kanta, sanye take da blue na hijab har k'asa sai niqab, bbu abinda kake kallo banda kwayar idanuwanta." gabansane yayi mugun fad'uwa tun rabuwarsa da *hanna* bai ta6a ganin wanda takwanta masa araiba sai ita,  bai k'ara tsintar kansa awannan yanayi ba sai yanzu, dukk da dacewa baiga fusknata amma taa kwanta masa."  ya nutsa cikin tunani harta tsari keke napep tafara tafiya." sai lokacin yadwo cikin tunaninsa yana kallo tafara tafiya yayi saurin bin bayqn keke napep d'in."
  Ganin andoshi angiwarsu *hanna* sanda gabansa yafad'ii haka harzuwa k'ofar gidansu, alokacin yagama cinkewa, besan waceec ba, sanun kansane ba *hanna* bane to wacece, ita?"
 Haka yayita zama awajen har kusan 1hour ganin bata k'ara fitowaba, yasashi jan motar yatafii."


  Waahe gari da 11:00am najeeb yaje gidansu *hanna*  yadad'e ak'ofar gidan yana jira ko zata fito amma shiru."  yakusan 3day's yana zuwa amma duk da haka bai ganinta, hakan yasa kawai yashare yacigaba da al'amuransa, amma kuma bawai dan yamanta da itaba yasa rai duk ranarda yaganta, in sha Allah sayya yi mata magana ."

   _Plz kiyi hakurii da jina shiru kwana biyu, wasu y'an matsalolii ne amma nagode, da kiranku da massg d'inki, kj kwantarda hankalinku lpyna klau kawaidai y'ar matsalace."_

 _Kujira na dare yau biyu zanyi_

   To be contiuned

Ur's z33yy bawa

*BIBIYATA AKEYI*

_Bismillahirrahmanirrahim_

Writing by
      © _Zaynab Bawa_
 ( _z33iiyyb3rw3r_ )

_Like my page on Facebook :::Zaynab BAWA novels_

Followed me on instagram ::::mhiz_z33iiyyb3rw3r

   *Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agareshi yace, "  *laula an aahukka ala ummatii*  yace dabadan zan takurawa al'umma taba yace, ```la'artuhum bissuwak inda kullil salat```  *yace dana umurcesu dayin aswaki ako wace sallah."   yin suwak babbar sunnace ta Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agareshi, yanadakyau bin sunnonin Manzon  Allah Allah kabamu ikon bii."*

   *Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agareshi yace, " kullaa ummatii yadkulal jannata illa man abah, duk alummata zasu shiga aljanna, harsai wanda yak'ii, mamaki yaakama mutanen dake wajan sukace ya rasuliahi yanzu waye zaiqii shiga aljnnah?"  sai Manzon Allah yace wanda yamun biyayya tabbas zaishiga aljannah, sannan yace wanda yasa6ani kuwa to tabbas yak'ii."     Allah kabamu ikon yin biyayya ga manzonka."*

  ================

*Wannan shafin nakune ku kad'ai, sanda nijar, da QUEEN, nagode da k'aunarku garenii nijar inasonku sosai."  ILYSM."*

Page   74

    Washe garii *hanna* tataashi dasauk'in damuwarta, amma wani shafin na zuciyarta yana fargaban halinda yake ciki, idan kuma tayi tunanin hakan Sai tayita addu'a." hartajii sanyii acikin zuciyarta, haka har aka shiga sabon satii."  anty afeeya kuma bata tafii ba, dan ita tafiso tatafii tareda *hanna* ."  Washe garii tun sassafe *hanna*  kwalliiya sosai ta shiga kitchen da kanta ta shirya masa abincii."  sosai tayi kyau."  zuwa yamma jikin *hanna*  yayi sanyii sosai."  anty afeeya dake zaune agefe tana kallonta tun d'azu gabaki d'aya tausayinta yagama kamata."  ganin magrib ta doso yasa         *hanna*  tajuya ta kalli anty dake zaune cikin alamun karyewar zuciya, da rawar murya da sark'ak'iya tace anty haryanzu shiru bbu labarin dawowarsu."
   Girgiza kai anty tayi tace, a'a *hanna*  kada kiyi kuka kinsan fa ba rana aka yankeba kuma ba sanarwa akayi ba, tom ki yi hakurii, amma kuma  mujirra zuwa gobe tukunna, ai shiru *hanna*  tayi batace komai ba."
   Har 10:00pm *hanna*  afalo tana zaune sanda anty afeeya ta takura mata sannan tashiga takwanta."
  Washe garii ma tun sassafe *hanna* ta tashi tafara aiki, kamata jiya sanda yagama komai sannan tashirya cikin ran tsattsen less mai kyan gaske."  tayi kyau sabon y'ar rawar ta tafara buya,"
  Anty afeeya da bata kallonta bbu abun da takeyi, duk tausayinta saiyabii yacikata."  yauma komar jiya *hanna* batayi baccin kirki ba."   sanda *hanna* ta shafin kimanin ten day's tanayiwa MG shirin dawowa amma bbu shi bbu labarinsa, ita kanta afeeya sanda tayi danasanin k'arya da tayi mata nacewa zasu dawo, tayi hakanne duk dan ta faranta mata rai."
   Washe garii suna zaune afalo *hanna* tayi mata shi ta cinyan afeeya suna d'an ta6a hira, yana tace tafara ringing dake hannun *hanna*."  ganin wandabekekira yasa jikin *hanna* yayi sanyii, dan tana mijinta ne, ita kuma nata mijin batasan awani hali yake cikiba."  nan take mood nata yacanja."
  Batasan mai anty afeeya ke fad'a ba hankalinta baya jikinta."  tana gama wayar tadubii *hanna* wanda hankalinta baya wajan tace *hanna* shiru bata amsaba  ta6ata tayi, firgitgit tataashi, Girgiza kai kawai anty tayi tace, *hanna* ki shirya yau muwuce nageria, abban adheel yakirani bayada lpy yanzu haka yana emergency, tak'arashe maganar cikeda tsantsan damuwa."  dasaurii *hanna* yatashi tace subhanallhi, anty tatashi tace anty adheel kuma?"
  Eh *hanna*  tashi ki shirya mutafii."  Girgiza kai *hanna* tayi hawaye na zirara tace anty kije kawai nikam zanjirashi." Girgiza mata kai anty afeeya tayi tace, a'a *hanna* bazan iya barinki anan ba."  tana kuka tace Allah anty bazan iya binki ba, wallhy zanzauna najirashi har iya k'arshen rayuwata,"  bayadda anty batayi *hanna* tabita ba amma tak'ii haka tana ganii takoma, ita kuma zauna zaman jiran MG."


================

   Karimace dake zaune tana yiwa abida masifa tace, wallhy nidai zantafii, kintsaya kina 6ata mana lokacii, kina so jimawa kad'an *mama tace tafasa."
  Itakuwa abida santa tagama iya shegenta sannan suka futa suka samu hafsat dake jiransu."  futa sukayi zuwa gidan anty, idan kagansu baza kace ba y'an uwa bane, iya kulawa ana bawa su karima, dan bbu wani bamabamcii, soyayya sosai suke samu daga iyalan gidan."  iyakacin soyayya mama tana nuna musu, duk kwakkwafin mutum bazai gane ba ita ta haifesu ba."  Itakuwa."  suma sun riqeta gamm tamkar mahaifiyarsu."
  Gidan suka nufa, suna shiga suka sami antyy maman amal nazaune, da sallama suka shiga abida tak'arasa gefenta da gudu tazauna."  dan jininsu yahad'u sosai."
   Rabon najeeb da gidan anty, tun auren *hanna*  dan fushi yakeyi dasu daga ita har mijinta, aranar kawai yajii sha'awar zuwa gidan kai tsaye gidan ya nufa."

============

Yau duk eatate yad'auka, gidan tv da radio Sai sanarwa ake da dawowan soldier's gobe, ai kuma farin ciki da fargaba duk yataruwa *hanna*   tanason ganin mijinta amma batasan awani hali zata ganshii ba, batasan yana raye ko baya raye ba."

  _Nacika alqawarii_

To be continued

Ur's
    Z33iiyyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*

_Bismillahirrahmanirrahim_

Writing by
      © _Zaynab Bawa_
 ( _z33iiyyb3rw3r_ )

_Like my page on Facebook :::Zaynab BAWA novels_

Followed me on instagram ::::mhiz_z33iiyyb3rw3r

   *Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agareshi yace duk  wanda yakaranta* ```waraddal lahul lazhina kafaru bi zaigaizihim lam yanaluu khaira akafallahull mu'umininal qital wakanallahu qawiyan aziza```  *Allah zai kareshi daga sharrin kowani irin hallita,*

     *Allah subhanahu wata ala yana cewa, wala'iin shakartum la'azidannakum, yace idan kuka godemin nikuma zan k'ara muku,  yanada KYAU fad'in kalmar Alhamdulillahi domin nuna godiyarka GA ubangiji. Koda ace Allah yajarabceka ta wata hanya, alokacin faruwar abun kalmar Alhamdulillahi ne kawai yakamata tafito abakinka A wannan lokacii." Allah yasa mudace ameen ya Allah*

================

  PAGE 75

*
   Kai tsaye gidan yayansa ya nufa, dan yayi kyewar gidan sosai, kobabu komai gidan na tariyo masa al amura dayawa."
  Yana isa yafito yabud'e gate kasancewar bbu mai gadii, ya shiga da motar sa, parking yayi sannan yafito yanufii k'ofar shiga gidan, entercorm ya danna, jin k'ara anty dake zaune tadubii karima tace je Ki bud'e kofa, bbu musu karima tatashi dake ita baimai surutu bane sosai."
  Hijab d'inta tad'auka tsumbulele har k'asa dake, dariya dukansu sukasa, anty tace saikace wata matar liman, cikin gidanma sai kinsa hijabii." abida ne tace anty rabuda ita Allah lokacinda muna gida gyallalukanta ma k'ananune."  juyawa karima tayi ta nufii k'ofa ta rabu dasu dan ita yanzu, tafison manya manyan hijabai, zuwanta bauchi yasa tajii tana sha'awar canja d'abi'unta, duk da tunda d'abi'unta ba munana bane amma tanaso na yanzu yafii nada kyau."   k'arasawa k'ofar tayi ta bud'e."
  Shikuma kansa na k'ofa yana jira A bud'e, tana bud'ewa sukayi ido biyu gaban kowanne daga cikinsune yafad'ii, saurin yin k'asa da kanta tayi tanajin wani irin yanayi tace, kashigo, shiru yayi yatsaya yana kallonta itakuma ta sunkuyarda kanta tana wasa da yatsun hannunta, tunanine fall aransa yasan shakka bbu ita ce wannan yarinyar dayaganii, kasancewar, yanayin daya tsincii kansa irinna ranar, hijabin ta irinna yarinyar ranar, kuma gashi yau yaganta a gidansu *hanna* yau awajen anty hakan yanuna sunada alaqa da ita kenan."
  Ganin yak'i cewa komai yasata juyawa takoma ciki, tana shiga anty tace wayene?"  cikin sanyin jiki tace umm anty bansan shiba, amma nace masa yashigo."   baisan tabar wajanba sanda yadawo daga dogon natsarinsa."  nisawa yayi sannan yace ya Allah kada ka jarabceni DA abunda zaifii k'arfiina, ya Allah kada kasa mun son yarinyar nan kamar yanda kasamun na *hanna* na azabtu da shii, Ya Allah kamun za6in alkhairii."
  Cikin sanyin jiki yasa kansa afalon had'eda yin sallama."    dasaurii anty tajuyo tace A'a uncle munyii fushi kakoma kawai, fara sosa kansa yayi yana dariya yace agafarcenii, kaina k'asa natuba, yana fad'ii yana k'arasowa."    dariya anty tayi tace dalili d'aya ne zanyafe maka." Dai-dai lokacin ya k'araso yana zama yace ai ahakanma nagode."
   Kallon abida anty tayi tace tashi kije kidauko masa drinks da abincii."   saurin tsaida ita najeeb yayi yace a'a barshi kawai nagode, wucewa zanyii nace barina biyo, 6ata rai anty tayi tace badai baka huce ba?"    murmushin dole yayi yace, ai dolena nayi hakurii, tunda bawani yajamunba."  nima kaina bansan dalilin yin hakanba,  jikin anty ne yayi sanyi tausayin najeeb yakamata, tace A Allah zaimaka za6ii mafii alkhairii, nisawa yayi baice komai ba."  sai alokacin suka gaisheshi ya amsa idanuwansa nakan karima, yatashi yace ni barin wuce, zandawo akwai maganar zamuuyii, toh sqika dawo kawai anty tace, sannan yatashi yafita."

================

   Jin dawowarsu MG yahana *hanna* bacci kwana tayi tana sallolii da addu'oii, har gari yawaye *hanna*  bata runtsa ba."
  Addu'a kawai takeyi, dakyar ta iya tashi tafara yiwa MG girki, sosai tagwada nata basirar, masu aikii dama kullum sukan shigo suyii gyara amma yau itada kanta ta tayasu suka Gyare ko ina sannan, ta turara gidan, kowani lungu da sak'o yad'auki kamshii."
  Shiga tayi itama ta fara nata wankan tadad'e tana wanka, sannan tafito turare kawai ta iya feshe jikinta dashi, amma ko powder kasa sawa tayi balle man le6e, fargaba tafii komai yawa aranta yanzu, doguwar riga ta zura, sai d'an kwalinta."  sannan tasauko palour ta zauna, bata dad'eba matar shahid taahigo dasaurinta tace, wa *hanna* ta tashi sutafii barrack, dan yanzu haka ance sun kusa sauk'a."  da Kallon tambaya *hanna* tabita tace dama banan zasu sauk'a ba."   girgiza mata kai tayi tace ainan gidajensu ne, zamuje taryanzu a barrack, mamakine yakama *hanna* ganin yanda bata damu sosai ba, hakan yana nufiin harsun fara sabawa kenan, waje sukayi sannan suka Shiga mota, ba'ad'auki lokacii ba suka isa."
  Sun shiga *hanna* *hanna* sai kallo take binsu dashi ganin yanda matan soldier's da y'ay'ansu, tako ina ta leqa matane da yara, kusan duk matan fararen fata ne, d'ai-dai kune blacks, sai kuma soldier's da suke barbarje a barrack d'in."   12:00 alqrm yabuga na jirgi yasauk'a, kowacce sai raba ido takeyi wasu matan kuma wak'a sukeyi, ba'afii 12:30 ba sojoji suka fara shigowa wannna wajen, wasu na shigowa riqeda akwatin gawa ahannun su."  sai sunshigo ciki su ajiye."  duk wanda tahango mijinta aguje suke tafiya su rungumesu, wanda suka hango akwatii da pics na mijinsu kuma wasu zubewa sukeyi ak'asa, wasu na ihuu tashi d'aya wajen ya karad'e ga sojojii basu fasa shigaba, *hanna* kuwa gabanta yafara dukan taraa tara idanuwanta sunkawo ruwa, banda hawaye bbu abunda yake zuba."
  Aikuwa can saiga abid ya shigo, yaronshine yafara hangoshi, jan hannun mamansa yayi yace momma momma yana nuna mata abid yace pappa, ganinsa sukeyi  gaban akwatin wata gawa, soldier's dayawa sun d'aukota da alamu ta babbane, nan gaban *hanna* ta matar shahid yafad'ii dan tabbas acikinsu mijin d'ayane."  kasa zuwa matar abid tayi dan daga alamu hankalinsa atashe yake, kowacce acikinsu raba idanuwa takeyi kozataga mijinta shiru bbu MG bbu shahid basusan wanene acikin akwatinba."  gashi basuga d'ayaba balle su tabbatar."  ganin an nufosu ne yasa zuciyoyinsu karyewa, har gaban, farisa sukazo matar shahid suka ajiye gawar sannan kowa yacire hulansa Aikuwa nan danan ta zube kan gawar tana kuka kamar rqnda zai fita zuciyoyinsu duk yakarye."  anrasa wanda zaiyi kanta ya rarrasheta, yaranta k'ananune amma sun fahimta nan suka fara kuka Awanna lokacii *hanna* itama kukan takeyi natausayin fariisa dakuma nakanta narashin sanin halinda mijinta yake ciki."  da guduu ra'iisa matar abid tashige jikinsa tana kuka, na tausayin y'ar uwarta, ita kuwa *hanna*  ganin sojojii sunfara k'arewa harsuka k'are, yasata farajaa dabaya, mai hakan yake nufii kenan? Badai wani abuu yasamii MG ba yana asibitii, rufe kunnenta tayi tafara kuka inaaaa hankainta bazai iya d'aukan wannan zance BA."
   Ficewa tayi tashige mota aguje, ta ce driver yatafii, suna isa bata barii yatsaida motarba tafice, aguje tashiga d'aki ta rufe kanta."  kuka takeyi kamar ranta zai fita."

      *NIGERIA*

  karfe 1:00pm Dai-dai, jet yasauke MG A cikin gidan sarkii, jin jirgii ya tabbatarwa iyayensa shine ya iso."    yana futa bai 6ata lokacii ba yashige shahin ummii ganin yanda tarame, ya bashi tausayi dasaurii yak'arasa yazube akan guiwarsa, ya rungumeta tsam, fashewa tayi da kuka, tak'ara k'ank'ameshi, dakyar ya rarrasheta ya saketa sannan yace, ummii na nadawo lpy dan Allah kidaina kukannan, share hawayenta tayi tace nadainaa, d'ana, tashi yayi yace barin shiga gun abba, dasaurii yatashi yafice dan damuwarsa kawai yawuce shahinsa yaga *hanna* , mai martaba yayi murnar ganin d'annasa, damacan yana boye damuwarsa ne dan yanda ummii kesaka damuwa ranta." 
  Baidade ba yafito ya nufii shahinsa ganin akulle abuu yabashi matukar mamaki juyawa yayi zuwa shashin ummii yasamu afeeyya har ta iso labarii ya isheta, ta guduu tatashi ta rumgumeshi tana cewa yaya ya baka fara zuwa wajan *hanna* ba?"  dagota yayi yace dama *hanna* bata dawo ba?"
  Gyada masa kai tayi tace yaya tak'ii dawowa, nan tafara bashi irin labarin damuwarda *hanna*  tashiga, sannan tace masa har ciwo tayi, ai nanda nan idon MG yakad'a, son *hanna* yana k'aruwa azuciyarsa, jii yakeyi kamar amafarkii wai *hanna* ne take wanna abun kansa," yawuce gidane domin ganin *hanna*  dan yanada ya'inin  bazata zauna zaman jiransaba, amma kuma yasamu sabanin hakan, juyawa yayi zai fice, ummii tace ina zakaje katsaya kacii abincii."  no ummii zan tafii wajan *hanna* bansan awani halii ta ke ba narashin ganina."  share hawaye ummii tayi sannan tatashi yariqo, hannunsa tad'auki wermer tadamka masa tace, kacii abincii ahanya Allah yamuku albarka, sumbatar goahinta yayi ya fice."
  Nan suka d'auki hanya dake jet ne k'arfe goma na dare suka isa, yana shiga alokacin *hanna* harta galabaita tsabar kuka."  yawuce sama yanda yaga wuta akunne alamu da mutum aciki."
  Dasaurii ya isa yana k'okarin bud'e kofar yajii akulle, da k'arfii yace, sweety am home, kamar amafarkii *hanna* tajii muryarsa aida gudu tatashi tabude, tana Kallon Sa atsaye da gudu tashige jikinsa, tana kuka sosai, har cikin jikinsa yakejin kukan,   cikin kukan tafara inasonka wallhy inasonka idan kasake tafiyya kabarnii zanmutu."  runtse ido yayi yanajin maganganun ta har cikin zuciyarsa, ganin takii daina kukanne yad'ago kanta, yahad'e bakinsu waje d'aya, ga mamakinsa *hanna* batayi kok'arin kwace kantaba sqima biye masa datakeyi."

   To be continued

Ur's
    z33iiyyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*

_Bismillahirrahmanirrahim_

Writing by
      © _Zaynab Bawa_
 ( _z33iiyyb3rw3r_ )

_Like my page on Facebook :::Zaynab BAWA novels_

Followed me on instagram ::::mhiz_z33iiyyb3rw3r
   
```Inna lillahi wa'inna ilaihi raji'un😭😭😭😭 Allah yajikanka Allah yarahamsheka Allah yasa aljannah ce makomarka😭😭😭😭😭 , dan Allah muna buk'atar addu'arku, Allah yayiwa lecturer d'inmu rasuwa, mal muhammad muhammad, addu'arku tafii komai mahimmancii``` 😭😭😭

   *Manzon Allah tsirada amincin Allah su tabbata agareshi, yace,"  ayatul munafiku na salatha, yace alamomin munafukai guda uku ne, izha hadatha kazaba,  idan yayi magana yayi karya, wato mak'aryacii yana d'aya daga cikin alamun munafurcii, kuma yace," wa''iza wa'ada aklafha, kuma idan yayi alk'awari yasa6a yanadakyau riqon alk'awari, domin mai karyashi Manzon SAW Allah yace mana munafiki ne, sannnan yace waizaa tu'umina kana, kuma idan aka yarda dakai kayi ka cii amana."   Allah katsaremu dacin amanar y'an uwanmu."*

    *Manzon Allah tsirada amincin Allah su tabbata agareshi yace,"  da'a ma yuribuka ila mala yuribuka,  kabar abunda kake kokonto akansa izuwa wanda bakada kokonto akansa, wallahu ta'ala a'alam, Allah shine mafii sanin gaskiya, Allah kasa mudace."* 

================

Page 76

*
     Sunfii 30minute ahaka, sannnan MG yasaketa, kollon fuskarsa ta tsaya yi har sanda ya hura mata iska a idanuwanta lumshe idon tayi sannnan ta sake bud'esu akansa, ahankalii takai kanta saitin dai-dai zuciyarsa ta kwantar da kanta, dasaurii-dasaurii takejin bugun zuciyarsa."  zagayeshi tayi ta hannayenta da k'arfii sannnan ta runtse idanuwanta."
Murmushi MG yakeyi yana k'ok'arin ganin fuskarta amma tab'oyeta cikin k'irjinsa."  ganin atsaye take ko motsin kirki batasonyii  yasashii sunkuyawa dai-dai kunnenta, yace heyy nadawo fa batafiya zank'arayiba, nokewa tayi tak'ara shigewa jikinsa, y'ar dariya kawai yayi aransa yanacewa yaushe *hanna*  tafara sonsa haka, yanayinta kad'ai yanuna irin damuwar da tashiga."  d'an rusuna tsayinsa yayi yad'auketa cakk zuwa cikin d'akin, har bakin bed yakaita ya zauna, sannnan itama ya zaunarda ita akan cinyarsa, k'ara shigewa jikinsa tayi, d'agota yayi yace bafa guduwa zanyi ba, girgiza kai tayi tace ni dai kawai kabarnii, Murmushi yayi kawai, ya sa hannuwansa yamata rumfa, rufff yarufeta a k'irjinsa, Haka suka zauna kowanne yanajin bugun zuciyar d'an uwansa, *hanna* jitakeyi batak'ii su dawwama ahaka har iya k'arshen rayuwarsu ba."  kaiwa bakinsa yayi dai-dai kunnenta, yace sweety inaso nayii wanka, d'agowa tayi ta dubeshii sannnan tace nikam bazan sakeka ba."
  Lumshe ido yayi yad'an tsotsi lips d'insa yace, tom aiba damuwa saimuje muyii tare," dasaurii tad'ago kanta ta dubeshii, tace nifaa Allah wasa nake maka zansauka, tafad'a tana k'ok'arin sauk'a,"  riqeta yayi gamm yace aikuwa sai kinjee, yana fad'in haka yamiqe da ita yanufii toilet, tana wutsil wutsil amma bai diretaba sai cikin toilet, yana ajiyeta yafara k'ok'arin rage kayansa, saurin juyadda kanta gefe tayi ta runtse idanuwansa, sanda ta tajii k'aran ruwa ta tabbatar ta yafara wanka tafice da gudu, sauk'a k'asa tayi d'an tanadar masa abunda zai cii."  snacks da tayi kawai tasamu ta d'auko da drinks wanda tayi da kanta, a cikin d'akin tashiga ta ajiye masa, sannnan tafice dan girka masa abunda zai kama cikinsa."  kitchen tashiga tafayii masa abincii mai squk'ii wanda zaicii dawurii."  30minute tafara yin  abincin harya kusa kammaluwa, d'aki tashiga dan ganin koya fitoo amma har lokacin bbu shii bbu labarinsa."  komawa tayi sanda abincin ya kammala tazuba ay'ar karamar cooler tad'auka tayi sama, tunowa tayi bbu plate takoma tad'auko had'eda spoons da serving spoon tayi sama, sai alokacin tasamu ya fitoo, kallonsa tayi tace kafa kusan 1hour a bathing kawai, yana goge knsa da k'aramin towel bai d'agoba yace, sweety yazama dolene nayii wankan samada hour, kinsan nakanyii satii acan banyii wankaba, riqe baki *hanna* tayi sannnan ta zazzaro ido tace, 1 week fa kace, lallai kazama, d'agowa yayi ya6ata rai, ai lokacii d'aya tayi shiru yace nazama mehh."
 Had'iye miyau tayi tace kazama jarumii, Murmushi yayi sannnan ya girgiza kai yak'arasa jikin dressing mirror, ganin bbu manda yake shafawa yasashi sauk'a k'asa, dan nemosu, baifii 15minute ba saigashi yadawo, bud'e k'ofa yayi ahankalii yashigo, kamshim da *hanna* tadad'e batajii bane yaziyarcii hancinta, harwani lumshe idanuwa tayii, tak'ara bud'esu sannan tajuya zuwaga k'ofa."  da Murmushi ta taryeshi harya k'araso, zama yayi kusada ita, yajawota zuwa jikinsa yace, wato nikike shirin cewa kazamii ko, yafad'a yana d'aga girarsa d'aya, girgiza kai tayi tace nifaa ba haka naceba ba, tafad'a kamar wanda maganar take tsoron  maganar, kamshin turaren MG ne gabaki d'aya yake fisgarta."  to me kikace yafad'a yana shafo wuyanta, lumshe ido kawai tayi takwanta ajikinsa, sannan tace bakacii abincii bafaa, nisawa yayi yace tohh kin danneni yakike tunakin zancii abincin,"
  D'agashi tayi sannan tafara zuba masa abincin, kamshin abincinne yadakii hancinsa, lumshe ido yayi ya bud'e sannan yau zancii abincin matata kenan, d'aga masa kai tayi tacigaba da zubawa."  tana gamawa tasa spoon ta eba tafara kaimasa bakinsa, kwayar idanuwansa cikin nata bud'e baki kawai yayi tazuba masa."  Lumshe ido yayi dan dad'in abincin, sannnan ya bud'esu akanta, cikin muryar rad'a yace, i have the best wife, in this world." 
  Dariya kawai *hanna* tacigaba da bashi abincii yanacii yana santii yana gwada mata duk duniya bbu wanda yakaita iya girki, haryaciinyee plate d'in duka, drinks da eba nanma abaki tabashi, shima ya amsa ya shanye, sanda MG yai damm sannan *hanna* tabarshii, tana k'ok'arin miqewa yariqo hanunta yace sweetyyy, nasan kemafa bakicii komaiba, yunwa kikejii kicii abincii, shafa cikinta tayi tace tunda naganka sai najii na koshii, balle danaga cikinka yacika, sai nima nawa yacika,"  Lumshe ido yayi yanajin wani nishad'ii nashigansa yace najii amma duk da haka cikii abincii." Bbu musu tadawo ta zauna tafaracii shikuma ya k'ura mata ido kawai, batacii sosai ba tatashii ta tattarii kayan tayi waje."
Tabar MG yana tunani kawai wani dad'ii yakejii waishine yau *hanna* take tarairaya, jiyakeyi kamar amafarkii, afilii ya furta, ya Allah kasa kodaa mafarkii nakeyii kada nafarka har abada."
   Yana cikin wannan yanayin tashigo tasameshi tace, ka kwanta kayii baccii kahuce gajiya, afilii ya furta idanma mafarkii kikeyii kidena, danni ba baccii zanyiba kuma bansan ranarsa ba."
  *Hanna* tade yafahimcii mai MG ke nufii yasata, shigewa band'akii dan yin wanka, gabantane yake fad'uwa, tana fargaba amma kuma bazata iya yiwa MG gardama akan abunda yakesoba, ayanzu yanda takejin sonsa akowani gabbai najikinta."
   Tadad'e awankan sosai, tayi amfanii da shower gel kala-kala band'akin kansa kamshii yad'auka balle ita kanta wanda tayi wankan."
   Tafito tasamu MG yakwanta har yafara baccii, da sand'a tashiga dan kar tatasheshi, turare kawai tashafa da humra, sannnan tasa sleeping dress mai kaurii, light off tayi, sannan tanufii gado ahankalii takwanta taja bargo tarufe jikinta."
 Sannan tayi off na bed lamp takwanta,"  bata dad'eba baccii yafara d'aukanta, har baccin yafara nisa, can cikin baccii tajii wasu irin abubuwa kamar wanda, baccinta tacigaba dayii, can jin abiin yafarayin yawa yasata bud'e ido, duk yanda taso jurewa kada ta masa gardama abun yafaskara, dan ganin abunna MG nashirin fin k'arfin tunaninta, kuka takeyii tana dukansa yasaketa bataso amma, yakii kulata,"
 (Toh masu karatuu abuu yawuce tunanin *hanna* ma balle nii, aikuwa naja kafata nafuce a d'akin) jinna bugii mutum gamm yasanii juyawa dan ganin waye, y'an bibiyata fans naganii abakin k'ofa kowacce idanuwanta kamar zaifad'ii tsabar leqe, maman bayo, ameena da asm'au ne suka fara turanii waii saina koma nad'auko musu maiyake faruwa acikii, nikuwa nayii k'irmushishi nace  bazaniba."
  Da gudu na sauk'a falo nabarsu sai leqe sukeyii,"  na jona wayata acharge dan d'auko muku rahoton gobe, na kishingid'a akujera kenan, najii kamar magana a k'ofa, futa nayii dan dubawa, naganoo jamila gumel da ghana must go d'inta ahannu, waii ita adole saita shiga wajan MG da *hanna* tazo, dakyar naroki sojoji suka barta tashigo, aikuwa tawuce sama da gudu danjin kwafkwaf, nikuwa na kishingid'a dan hutawa."

To be continued

Ur's

   Z33iiyybawa

*BIBIYATA AKEYI*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

Writing by
     *©zaynab bawa*
*(Z33iiyyb3rw3r)*

_Like my page on Facebook=zaynab  BAWA novels_

 _Join my group on Facebook= ZAYNAB BAWA NOVEL'S_

  ```Manzon Allah tsirada amincin Allah su tabbata agareshi yace ,مانهيتكم عنه .فاجتنبوه وماامرتكم به, فاءتوا منه مااستطعتم فاءنمااءهلك الذين من :قبلكم:  كثرت مساءلهم واختلا فهم على اءنبياءهم
manzon Allah SAW yace abunda nahanaku to lallqi Ku gujeshi, kuma abunda na umarceku kuyi iya gwargwadon iyawarku, monzon Allah SAW yace yanadaga cikin abinda aka halaka way banda sukazo gabaninku, manzon Allah yace anhalakardasu saboda yawan yawan tambayoyinsu, da yawan sa6awa annabawansu, Allah kabamu ikon bin umarnin ma'aikinmu.```

================

Page.  77

*
  Zazza6ine mai tsafin gaske yarufe *hanna* ko idanuwanta wahalar bud'ewa yake mata, numfashii takeyii sama sama, Sosai hankalin MG yatashi,  har 9:00am bbu abunda *hanna* tacii, duk yabii yasusuce hakanne tasa shima bbu abunda ya'iya sakawa abakinsa, gas hi yanason fita zuwa asibiti Dan dubo jikin shahid, sai 9:30am kafin doctor daya Kira tak'araso, sugar a tayi sannan tace masa zazza6ine mai zafii, magan ganuwa tabata wanda dama already tazo dasu, dan tun awaya yamata bayanii."
  Miqa masa maganin tayi sannan tace tasha tasha wannan amma taci abinci tukunna, sannan layout Mata werming jikinta kamar sau huduh, tunda dama kace already kayii, godiya yamata sannan yarakata har bakin door ya juyo, Kai tsaye kitchen nufa, tea yahada Mata mai tsafii kozai sauk'ar mata DA zazza6in, sama yayi dashi, da salaama yashiga d'akin *hanna* ta amsa ciki ciki wanda data hqnkalinsa yana kantaba bazai Lura ta amsaba, kuma face dinta yana facing door ne." Karasawa yayi yazquna abed side drawer dake gefenta.". Ta6a jikinta yayi yajii haryanU da zafinsa rauu gawanii irin numfashi datake fitarwa mai tsafin gaske."   Ahankali yad'agota, sqnnan yakafa mata cup na tea d'in, kad'an tasha tanemi sake kwanciya bai bari takwanta ba sand a yabata maganii tasha, tukunna tad'an zauna nay'an minute's maganin yayi melting kafin yakwantarda ita."    Zama yayi shima agefen gadon yak'ura Mata idanuwa, itakuma nata yana lumshe da alamu bacci takesonyii.". Aikuwa bata dad'eba bacci ya ebeta, yakusan 1hour ahaka yana shafa fuskanta kawai itakuma sai baccinta takeyii, jin yanda numfashinta ya dai-dai ta, yasa hankalinsa yad'qn kwanta Dan yanzU bbu zafii kamar d'azu ,back hand d'insa yasa forehead nata danjin temperature nata, yajiih bbu zafii sosai sai d'an dumii Wanda dama normal jikinta yanada d'an warm temperarure."  Sosai hankalinsa yakwanta, miqa *hanna* tayi sannan ta Fara bud'e idanuwanta ahankali tasaukesu kansa Wanda dama tuntunii shi idonshi nakanta murmushi yaskar Mata itakuma dasaurii tamayarda idanuwant ta damke dan wata irin masifaffiyar kunyarace tarufeta." Y'ar dariya MG yayi sannan yace yajiki?" Idanuwanta na rufe ta turo baki tace bansaniba waro ido yayi yace ni in kike cewa bakisaniba?". Eh tafad'a hadeda murguda baki😚. Hmm aike matsoraciyane tunda saikin rufe idanuwa kike rashin kunyan, whatever Hanna tafad'i , hah MG yafad'i sannan yace wannan y'a bazata ta6a canjawa ba."
  Tashi muje ciki abincii, *hanna* Wanda har time d'in idanuwanta alumshe yake tace nakoshi, matsowa kusada ita yayi sannan yaje dai-dai kunnenta yarad'a mata mata wani a buy nidai bansan maiyace ba, ware ido *Hanna* tayi dasaurii tace muje toh toh, wani killer smile yasake, sannan yagyada Kai, amma zanyi,, saitayi shiru zakiyi meh?" Yaatambaya kuka tasa, squri yayi yafara lallashinta yace kiyi hakuri, fitsarii zakiyi?" Kai kawai tagyada masa, d'aukanta yayi cakk harzuwa toilet ajiyeta yayi tace kafita toh, bbu musu yajuya ya fice, sanda tagama tarasa da wani suna zata kirashi, kawai takwala ihuu, da gudu MG yashigo yana zuwa dasqurinsa yayi wajanta yana tambayarta meye meye faruu, batayi maganaba, sai hannu data miqa masa ta langa6arda kanta, alamun yad'auketa, tsayawa Yayi yana kallonta baice komaiba sai girgiza Kai kawai yayi yad'auketa har zuwa falo sannan ya ajiyeta akan kujera yana yad'auko abincin duk yanda yayi *hanna* taci abincii taqii,  jawota jikinsa yayi sannan
ya kwantarda ita yace, swety shahid fa ba lapiya Dan jiya antaho tashi bbu yanda yake
Ninawuce  Nigeria sukuma Sunyi hospital, tun d'azu nakeson zuwa dubashi amma bazan iya ragouts nabarki awannan halii ba." Gaban *hanna* yafad'i kaddai baisan cewa shahid yarasu ba." Muryar MG ne takatseta dayace shima dai yayi shirme da Narvik ajkinsa bai nunaba, harsaida jini maiyawa yazuba ajikinsa, haryakaiga bbu jini ajikinsa." Nisawa *hanna* tayi tarasa tayaya zata fad'a masa cewa shahid yarasu." Ahankalii tace nikam da shahid da abid wanne jininku yafii had'uwa, nauyayyan numfashi yasauk'e yace hmmm shahid yafii shiga rai, kinsan yafii son mutane, abid naira magana ,murmushin yak'e tayi tace, halinku d'aya kenan, Jan hancinta yayi yace ai yanzu kin koya mun, murmushi tak'arayi tace, amma acikin abid da shahid way a you Sonka?? Murmushi yayi yace ai daukansu suna sona saidai, shah I'd yafii hakurii da halina, jijjga Kai tayi tace tom, amma tsaanin kaida abid wayafii son shahid?? Dariya yayi yace, ehtoh aikinsa bansan zuciyar abid ba amma ai Nagaya miki shahid Nada shiga rairai, hmm hakan yana nufiin kafii sonsa kenan? Eh kawai yace atakaice, OK tom tskaninka da iyalanshi wayafii sonsa?" Jikin MG ne yayi sanyii yace sweety aike madai kinsan iyalanshi sash to I sonsa, job jijjaga Kai tayi, tafii 2minute bata Kara cewa komaiba, can sai tace tom yanzu da iyalanshi da Allah daya helix crank way at it sonsa?". Gaban MG neyafara fad'uwa, yafii 5 minute sannan cikin sanyin jiki  yace, sweety maiyasa zaki hada sonda muke masa dakuma Wanda ya halicceshi yake masa?"
  Kwantarda kanta tayi ak'irnsa sannan tazagayo da hannayan ta zuwa bayansa tariqeshi dakyau sannan tace duka Wanda yafiku sonsanne yakarbi abunsa,
Runtse ido MG yayi Yanajin zafii cikin ransa, lokacii d'aya idanuwamsa suka kad'a sukayi Jannie, jiikinsa har 6ari yakeyi, mayseta Yayi ajikinsa sanda tadanyi K'ara, neman hawayensa yayi yarasa yayinda *hanna* keta nusardashi akan hak'urii, yafii 25minute awannan yanayii ba abinda ya iyayii ,hawaye yakeso kokad'an yazubo masa amma yak'i zubowa, zuciyarsa kawai ke masa tukuk'i."
  Ahankali *hanna* tamiqe tazauna Dan zamanma dakyar takeyinsa, tana runtse idanuwa ta dubeshi tace, kajeka kar atafii dashi bakanan. " dagowa yayi yadubeta da idanuwansa jawur yace, we are frnd for over 28yrs ,Hanna yakike tunanii zanjii araina, am dying inside yafad'a yana nuna zuciyarsa, nan danan *hanna* tafara kuka, amma MG idanuwansa akafe suke, riqe kansa yayi, ta matso kusadashi ta jawoshi jikinta tana shafa Bayansa,
  Akunne tak'arace masa kaje asallaceshi dakai, d'agowa yayi yana kallonta kamar Maison gano wani abuu, magana yakesonyii amma yakasa,  yabud'e baki zaiyi magana taxi saurin sa hannunta Abakinsa tace, shhhh I will be okay, just go." Baiyi magana ba ya sunkuceta, har sama yakaita ya ajiye akan gado, sannan shikuma yashirya ajiye mata duk wani abunda data buk'ata akusada ita sannan taugunna yamata Peck a goshinta yamata light kids q goshi sannan ya fice izuwa wajanda zai samuu shahid."
  .

================

  Najeeb ne yashirya Dan she's gidan anty, karfe 10:00am ya isa gidan, dama anty taasnda zuwansa ,bayan sungama gaisawa ya kalleta yace ,anty nifa DA bukata maxi, mirmushi anty taxi tace fad'i mana inajinka Sosa Kai Yayi yace anty bbu wani boye boye ,wallhy 6ta d'inki Wanda tasa dogon hijab dinan nakeso, sauke ajiyar zuciya anty tayi sannan tace."

   To be continued

Ur's
   z33iiyyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

Writing by
     *©zaynab bawa*
*(Z33iiyyb3rw3r)*

_Like my page on Facebook=zaynab  BAWA novels_

 _Join my group on Facebook= ZAYNAB BAWA NOVEL'S_

*Manzon Allah tsira DA amincin Allah su tabbata agareshi yace, Ku kasance masu yafewa y'an uwanku laipukansa, sannan yace Ku kasance masu yiwa y'an uwanku kyakkaywan zato.". Allah kabamu ikon yafemu y'an uwanmu karakuransu," ameen ya rabbil izzat*

.
================

  Page 78

*
     Nisawa anty tayi sannan tace, najeeb nima zanso hakan dan karima ta cancanci asota, karima tahad'a duk wani halida za'ayi sha'awa to karima tahad'a shi, sannan xan taimaka maka harsai ka aureta ,wani farinciki ne ya lullube najeeb jin yanada kwarin guiwar wajen anty,
  Nisawa anty tayi sannan tak'ara cewa   amma yanzu Vanda ikon isarda Kai gunta harsai randa *hanna* tadawo."
Cikin saurii najeeb yad'ago yadubii anty yace menene had'in *hanna_* aciki? Dahar za'ace saita dawo, girgiza Kai anty tayi sannan tace ba haka bane kada kamun guguwar fahimta, shiru yayi sannan yace toh anty menenen dalili?  Kayi hak'urii najeeb bazan bazan iya fad'a maka dalilibq amma inaso kasan cewa tabbas dalilina mai kwarin gaskene,  girgiza Kai najeeb yayi sannan yayi biting lips d'insa yace, anty kimin iso wajansu mama nizan Mata bayani, jijjiga kai anty tayi sannan tace, kayi hak'urii najeeb bbu abunda su mama zasuyii akai har indai bawai *hanna* bace tadawo, wani zafaffen numfashi yafutar sannan yace zanjirata ,zanjira dawowar *hanna* amma anty dan Allah kisa yaya yayiwa Abba magana, yak'aramun months akan way'anda yabanii, in sha Allah zanmasa magana sannnan zansan yanda zanyii na had'aku da ita amma kada ka mata maganar soyayya kawai shakuwa tashiga tsakaninku , itama kanta ba samun hankalinta zakayi ba, harsai *hanna* tadawo, runtse ido yayi yanajin zafii wai yaga abunda yakeso amma ace sai *hanna* tadawo." Maganar anty ne takatseshi dacewa sannan kuma plz kada ka tambayeta ita wacece kokuma wanene iyayenta, kamin alfarmar wannan, jijjiga Kai yayi kawai sannan yace nqgode." Murmushi kawai anty tayi sannan tace bbu komai, bai dad'eba yatashii ya mata sallama yatafii."
 

   K'arfe 8:00pm dai-dai, anty takira mama, hassana ce Wanda wayar mama ke hannunta tazo da gudu ta miqawa mama phn tana hakii tanacewa mama Ana kirankii, dasqurii mama takar6a sannan tayi riceiving, gaisheta anty tayi , mama ta amsada lpy ya yaran?". Lpynsu klau cewar aunty, shiru tayi, nad'an wani lokacii, mama dake tana fahimtar yaranta akowanii hali suke tace, wata matsace, yanayinkii yanuna kinason cewa wani abuu, umhm uhmm dama mama karima nakeso inzo ind'auka takwanamun biyu, mama aiki yanamun yawa, shiru mama tayi sannna tace, fatee kina mace kice  aiki yamiki yawa, shiru tayi sannan tace mama wallhy zama ni kad'ai ne yakemun yawa, mama kinsan su amal suna gidan kakansu, shiru mama tayi sannan tace fatee kinsan anama d'ayace bazan hanaki karima ba amma kikula da ita, godiya anty tayi sannan suka gama sallama."
  Ta ajiye wayan baifii da 10 minute ba, kiran *hanna* yashigo dasaurii mama ta amsa danta dad'e bayaji muryar y'artaba, kuma kota kirata baya shiga, gaisawa sukayi nan jikin mama yayi sanyii yanda tajii muryar *Hanna* tace *hanna* wani abunne yasamu abdullahin?" A'a mama bbu abunda yasameshi ,abokin sane yarasu, eyyer Allah yajikansa to DA amin *hanna* ta amsa Sun dad'e suna hira mama tana Mata nasiha sannnan sukayi sallama."

   Kilishine zaune afalo kana kallonta kasan tana cikin tashin hankalii, " intisar na zaune agefenta, itama ranta abace, kilishine tace, shashashar yarinya tunfarko basanda nace miki kibarnii naje wajanda za'a jawo hankalinsa jikinki ba, kikacemun wai kinsan abunyii, gashi jiyaa yadawo ko sallama baiyiwa mahaifinsaba, balle mu musamu gaisuwa yakoma, idan kikace nabarki da dabararki yanzu me dabararkin yayimana?" Ai amfad'a abunda babba yahango yaro ko yahau rimii bazai hango ba." Sunkuayrda Kai intisar tayi zuciyarta tana mata suya, itadai tanaso MG sosai kuma duk yanda za'ayi saita aureshi bazata taba barinsa ma wannan munafukar  yarinyarba nisawa kilishi tayi sannan tace Yanzu haka tun shekaran jiya anakar6o maganii yayi aikii akansa sosai, sannan yace, harsai sundawo zanzuba musu a abincii, anan zasu fara samun sa6anii, kad'a kai intisar tayi tace, wallhy umma sune sai shagen taurin Kai sekiga anyii abun amma kamar ba'ayiba."
   Yanzudai mubar komai harsai sundawo tukunna." Amma dai bazan fasa aika musu da abubuwa ba, amma yanzu kikirashi ki gaidashi tukunna a, kada kinuna masa komai, dato kawai intisar ta amsa."
 

================

  Yana isa yayi duk wani step dazq'abi Dan samun gawar yabii, tukunna, yasamu akabashii, ganin irin halinda yake ciki, yasa duk cikin soldier's dinanna bbubwanda ya tunkareshi koda maaganane, damuwa awajen MG dolene dan yayi rashin abokin arziki, tunda ya isa wajan bbu Wanda yakula kuma bbu babu, KO magana kasa yinta MG yayi idanuwansa sun rine, barin yanda yashiga yasamu matar da yaran kuka kawai takeyii."  Gabaki d'aya ta zabge, iyayen shahid sunyii waya tun jiya akan akawoshi su binneshi dakansu, alokacin aka fara preparation nazuwa k'asar india dake asalinsa dan canne,"
   MG yaso yakoma gida Dan sake kallon *hanna*  amma abun bai yiwuba, tako Ina ka kalli sojoji zaka gansu DA farin kyalle d'aure a hannayensu. "
   K'arfe 1:00pm dai-dai jirgin sojoji da dama yatashi Dan Kai way'anda suka mutu k'asarsu."
  MG basu gama yin jana'iza na shahid ba saida dabb magrib, bayan sungama yanemii ganin matar shahid koda wata matsala shi zai wuce, yananan ne amma hankalinsa yana wajen Hanna, baisan wanii halii take ciki ba."
  Tare aka musu iso shida abid dan shima matarshii tana ciki. " sanda sukayiwa iyayensa Mata naciki ta'aziya sannan suka wuce wajan matan, koda suka shiga sunsami, matarshi yanzu da d'an saukii saidai sharar hawaye datakeyii, kowanii lokacii, bayan yamata ta'aziya ne yake ce Mata ko akwai wani abune zai wucene, girgiza masa Kai kawai tayii." Bai dad'eba yafitoo yakamo hanya dake jirginsu na sojojine yayi saurii sosai. " cikin dare suka isa sosai, yana shiga d'akinda take yanufa,  yana zuwa yasameta kwance bacci takeyii, sauk'e ajiyar zuciya yayi yakarasa wajanda take, jin yadda take numfashii dakyar yasa yakai Hannunsa jikinta zafii yajii rauu, nan hankalinsa yatashii, zazzabin yadawo kenan,".  Zama yayi kusada ita, jin zaman mutum yasata bud'e idanuwa komardasu tayi ta rufe, amma kuma tagane wayake kusada ita,". D'agata yayi yace tashi muje kiyi wanka, yana fad'in haka yayi toilet da ita, wanka yamata sannan yafito yahad'a mata ruwan zafii, dakyar *hanna* Tasha sannan yabata maganii," kwantarda ita yayi shima yashiga yayi wanka, yunwa yakejii sosai Dan tun safe bbu komai acikinsa." Kitchen yanufa dan yasan yasan, baza'arasa abunda zai Ciba, yaban yad'anci ne yajuya zuwa d'aki kwanciya yayi a kusada *hanna*  baidad'eba shima baccii yad'aukeshi."
  Bashi ya farkaba harsaida aka Kira sallan subh, sai bayan yayi yatashi *hanna*  itama dakanta tashiga tayi alwala sanna tazo tagabatarda sallah dan yanzu zazza6in yasauka, Sallah tagabatar itama sannan fajitas zuwaga MG tace masa inakwana, murmushii yayi ya amsa da lpy, sanna tace ya hakurii Allah yajikansa da amin kawai ya amsa,  sunfii 10minute bbu Wanda yak'ara cewa komai, kallonsa tayi sannna tace, idan garii yayi haske zanje gidan rasuwan, kallonta yakeyi  ta kasqn ido yanda take maganar kamar akwai yanda yake Mata ciwo, yace ai suna can k'asqrsu, Dan iyayensa sun bukaacii akaishi can." Can kaje jiya?" Ta tambayeshi d'aga Mata Kai kawai yayi, Aida baka dawo ba, kaga duk zasu zquna amma banda Kai, sa hannu yayi yajawota daga yanda take zaune yace, tayaya hankalina zai kwanta nabarkii awani hali uhum? Runtse idanuwa taxi sannan tace tom mukoma yau, saikin warke yace atakaice, dasauri tace nawarke muje kawai,  zamuje amma sai zuwa yamma, zamu d'auki hanya yafad'a jin haka yasa bata k'aracewa komaiba.".  Yau jikin *hanna* dasaukii hakanne yasa suka shirts Dan zuwa India, k'arfe hud'u na yamma jirginsu yatashi. "

  To be continued

Ur's z33iiyyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

Writing by
     *©zaynab bawa*
*(Z33iiyyb3rw3r)*

_Like my page on Facebook=zaynab  BAWA novels_

 _Join my group on Facebook= ZAYNAB BAWA NOVEL'S_

    *Manzon Allah SAW yace," izha dakhala ramadana futihat abwabal jannat, agulliqat abwabannar, wa sulsulatil shqidhan."*  *(idan Ramadan wata mai albarka mai alfarma yashigo, Ana bud'e k'ofofin ajannah, sannan akan rufe na wuta, kuma akan mille shaidhanuu.)* *Ya Allqh Allah kasa mudace , ameen ya Allah.*

   *Manzon Allah SAW yace, izha nasiya waj akhala au shariba ,fal yutimmu sawamahu, adh'amahullah," (manzon Allah yace har indai kayi mantuwa kacii abincii ko kasha abinsha kana azumii kacii gaba DA azuminka Allah ne yaciyar dakai)"*
 

.

================

Page 79

  Sai cikin dare suka isa, dake dama tun tuni sunsan da zuwansu, shiyasa matar abid tajirata shikuma yatsaya wajan abid, sossi *hanna* ta tausaya matar shahid ganin irin halinda tashiga, ta rame gabaki d'aya ga yaranta biyu,"   duk wani kulawa dayakamata suna bata dukda itqka *hanna* bawani lpy ce DA ita sosaiba, zamansu awajanta yasa gabaki d'aya tasamu sukunii, shikuwa MG kamar akan k'aya yake jinsa kasancewar bbu *Hanna* kusa dashi arana baifii yaganta sau biyu ba, hakanma sai indai yashiga, itama *hanna* anata wajen hakan abun yake, daurewa kawai takeyi, amma tayi missing d'insa sosai,
   Anayin 7 da rasuwar, duka sukayi shirin komawa, sosai hankalin matar shahid yatashii nan wani sabon kuka yataso, tausayinta yasasu duka kuka, kukan rabuwa sukeyi sosai Dan kowanne yanajn d'an uwansa ajiki dakyar suka rabuu nan flight ✈d'insu yatashi zuwa Russia, kowa dakewar d'an uwansa cikin jinin jikinsa." Suna cikin jurgi MG yamaida hankalinsa kan *hanna* Wanda ta lafe ajikinsa kamar marar lapiya, yasan cewa duk zafin rabuwada matar shahid ne ke damunta, dan shima kansa ya lurada yadda sukafii shak'uwa fiyeda matar abid." Cutie pie😍 yakira DA sanyayyan jiki ta d'ago ta dubeshi, sorry yace, d'an motsa bakinta kawai tayi batareda tace komaiba, yace kingafa nayii loosing frnd d'ina ,he's gone forever amma nayi hakurii, kuma kene kika nusardanii, kema kiyi hakurii kinjii?" Gyada mishi Kai kawai tayi yace, kumafa Baku rabuba, anytime u wsh to see her, Zan kawoki, kinjii, d'ago kanta tayi tace promise?" Lakatan hancinta yayi yace yeah promise habibty,". Kwantarda kanta tayi akafad'ansa, can kuma kamar wanda tatuno wani abun,cikin muryar shagwaba tace, kada ka sake kirana sweety, zaro idanuwa😳 yayi yace why dear?"
Cutie pie sound better tafad'a tana jijjiga Kai, dariya yayi kawai yace ur wish."
  Harta kwanta tak'ara tasowa tace and habibty, auhhhh tayi kamar mai shirin yin amai tace never, an then why? again ya tambaya, yatsine fuska tayi sannan tace u called that Bea,,,,,,  saurin saurin rufe bakinta🙊 tayi, zqro ido😳 kawai yayi yana kallonta, wai intisar kike nufii? Whatever ni bansonjin sunanta aika kirata habibty, jawota jikinsa yayi sannan ya lakato hancinta ,turo bakii tayi,sa hannu yayi yatura bakinta, yace, wannnan matar nawa tafiya kishi, murgud'a baki tayi tace aikai d'inne dole ayi kishinka, wata murmushi ne yasu6uce masa harsanda  kumatunsa suka lotsa, d'aga gira d'aya yayi yace cutie do u love me that much? Itama d'aga giranta tayi idanuwansa yana cikin nata tace, yeah i do, I luv u then, now and I will love u forever."  Hure idanuwansa tayi ya lumshesu, numfashinsu yana dukanna juna ,tacigaba da cewa, kuma bazan daina sonkaba har iya k'arshen rayuwata, kowanne numfashina da sonka yake futa, lumshe ido kawai yayi dai bbu wata kalmarda zata nuna irin farincikinda yake ciki, wai daga bakin *hanna* suke futowa, jingina yayi da kujera Ya lumshe idanuwansa,  d'an k'ara tsawonta tayi takai dai-dai fuskarsa, saukan numfashinta yajii akan fuskarsa hakan baisq yabud'e idanuwa ba, dan farincin dayake ciki bazai iya barin idanuwansa abud'e ba, bakinta takai dai-dai nasa, sumbatarsa tayi sannan ta kwanta akafad'unsa ta saqalo hannayensa." Ahaka har suia isa, bayan sun shiga  gida, d'aki *hanna* tawuce kayan jikin ta ta rage dan shiga wanka, bayan tafito ne tazquna tana jiransa ko Ina yatafii ohow tafad'a itakad'ai, kwanciya tayi abunta, amma Sam baccin yak'i d'aukanta, tunani takeyi Ko Ina yaje?"
  Keep mawa tak'ayi takwanta amma bbu bacci  bbu alamansa, tun dawowar su fa bai shigo ba."  Sauk'a falo tayi tazauna akan kujera tana kallon k'ofa ,tafii 2hour's dazama sannan yashigo, DA sallama yazauna kusada ita, kallonsa tayi ta marairaice tace Ina kaje?" Kardai kindamu?" Batarai tayi tace au tambaya tama kakeyi, kaida kasan dole nadamu cikin wasa yace toh tafiyata ya kikayi, all alokacinda yake mutuwa ko rayuwa, mood d'intane yacanja, tace sau biyu fa Ina kwanciya a asibitii Kai baza kagane bane, zaroo idanu yayii yace, serious fahh, yaushe kika fara sona haka?" Nima kaina bansaniba, amma lokacinda nayi noticing hakan shine  lokacinda nasan irin sonda kakemun." Lumshe ido yayi yace cutie intambayeki mana?"
Ehem inajii ta fad'a, Lokacinda kike nuna baki sona, cutie dagaske ne baki sona."  Ta6e baki tayi sannan tace not really kawai dai am not into u, kuma ni lokacin banson Namijinda yafii ni kyau ne that's all, Dariya MG yayi mai isarsa haryana riqe caki yace ked'in wayace moki nafiki kyau?"  Haushine yacikata lallai wannan mutumin ya iya rainin wayo, afili tace au sai anfad'a munne ni banida ido ko?" Sorry bahaka nake nufii ba cutiee, Allah kuwa banfiki kyau ba." Kallon galala tamasa, lallai wannna guy d'inma, tashi tayi fuuu zatabar wajan, saurin kamo hannunta yayi, yazaunarda ita akan cinyarsa yace walhy Allah u r most beautiful gal I have ever seen in my entire life, tunda nake idanuwana basu ta6a ganomin wata mace amatsayin mata ba." Bakinta tasa akan hancinsa tana wasa dashi ahankalii bai ankaraba sanda ta garya masa cizo tatahi aguje tayi d'aki tana dariya, girgiza Kai kawai yayi yabita abaya, samunta yayi harta kwanta ta kud'unduna abargo, wanka kawai yashiga yaban yafito yadubeta yace heyy bud'e idanuwaki muyii magana, bbu musu tatashi tazquna tace inajii, zamutafii Hutu gobe da murnarta ta miqe tsaye tana cewa dan Allah gobe zamu koma gida?"
Umm Umm ba gida zamu komaba yawo zamu tafii ko Bali so, murnarta tad'an koma ciki kad'an tace little better, but promise me, muna komawa da 1day zaka kainii wajen mamana, promise kawai yace, itama tace OK agreed, amma ina zamuje?
Sai yanda kika fad'a cutie ur wsh is always my command, nikawai kaza6a kasan bayanda nata6a zuwa, amma zamuje umrah ko,wannan yazama tabbas yabata amsa, an then saika za6a, ok karki damu gobeda safe zamu wuce."
  OK tom, kawai tace  takwanta shima kwanciyar yayi yace, baidad'e DA kwanciya ba yajawota jikinsa, nidai daganan bansan maiyafaruu ba dan fucewa nayii."
    Sassafe suka Kama hanyar Duba abu-dhabi,  a burij al'arab hotel suka sauk'a, tsakanin MG da *hanna*  soyayya akeyi natshin hankali, kowanne yamanta da damuwarsa, idanka gansu gabqki d'aya sun murmure kowannen su hard'an qiba Yayi, satinsu days, a burij-al'arab sukayi shifting to burij kalifa, kwance suke ad'aki *hanna*  nakwance akan qirjinsa ta d'ago kanta ta dubeshi tace, honey boo ni ba'anan dangin ummii suke bane?"
Anan suke me kika ganii?" Dukan qirjinsa tayi sanda yace auchhh menayi?" Shine kak'i kakainii kanaso ace bansan dangin mijina KO?" No bahaka bane nasan yanzu ko munje zasu riqe kine, nikuma bazan juraba, Dan hakaa kibari kawai, saura kwana biyu, sai muje can, hakan kuwa akayi saura 2day's, sukaje gidansu ummii  iya soyayya *Hanna* taganta ,kamar zasu goyata kowanne burinsa yafaranta mata, wani lokacin abinci maman ummii ke bata abaki, *hanna* bata tashi taga kakaninta ba amma kuma tanajinsu ajikinta sosai, soyayyarsu takejii aranta, kwanannsu biyu sukayi haramar yafiya, kowannensu sanda yayi missing d'inta Dan sun shaqu sosai. "
K'asashe dayawa suka halarta, k'qrshene suka nufii saudii dan gabatarda umrah, sunyi ibada sosai, yayinda shikuma MG burinsa, dayayita roqa akan Allah yabasu zuri'a dayyiba,". Satinsu d'aya suka nufii Russia Dan gabatarda wani taroda za'ayii,  Ana saura kwana d'aya taron suka isa, can washe garisassafe za'a fara, ganin shahsin abid abud'e yahana *hanna* shiga dasaurii tayi hanyar gidan, tana zuwa suka bud'e Mata tashige aguje, afalo tasameta suna kallon juna da gudu suka rungume junansu."  Kuka suka sake dukansu, dakyar suka sake juna, kallonta matar abid tayi tace irin wannan qiba haka Anya bbu ajiya acikinann, dariya kawai *hanna* tayi tace bbu komai nikam, zama sukayi suka shantake tad'ii kawai suke yi." Itakanma  tamanta d MG sanda dare yayi sosai sanda ya kiirata tukunna tatashi." Washe garii kuwa tun asuba garin yafara cika duk wasu manya da shuwaga bannin kasashe sun hallara Kama daga manyan sojojii lauyoyii, police."  Mutane Kala Kala," cikin shigar sojojii plane green yadii nasu, MG yayikyau, sosai fad'in irin kyawunda  yayima 6ata time ne, itakuwa *Hanna* green d'in atampha tasaka mai ratsin farii, sannan tasaka green na gyale, sosai itama tayi kyau, motocinsa suka nufa, nan suka d'auki hanyar wajan taron."

To be continued

Ur's
    z33iiyybawa

*BIBIYATA AKEYI*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

Writing by
     *©zaynab bawa*
*(Z33iiyyb3rw3r)*

_Like my page on Facebook=zaynab  BAWA novels_

 _Join my group on Facebook= ZAYNAB BAWA NOVEL'S_

   *Wani Sahabi ya ke cewa wata rana muna tare da Manzon Allah Sallallahu Alaihi wasallama sai wani mutum daga cikin sahabbai ya ce Allahu Akbar kabirah, Walhamdulillahi kasirah, Wasubhanallahi bukratan waasilah, Sai Manzon Allah ya ce wanene cikin ku ke fadar wannan kalma, sai ya ce ni ne Ya rasulullah sai Manzon Allah ya ce nayi mamakin wadan nan kalmomi da ka fada, anbude kofofin sama gaba daya saboda wannan kalma da ka fada.  Sai Abdullahi Dan Umar ya ce tun daga wannan rana kullum sai na fadi wannan kalma, ban taba tsallake wata rana ko wani lokaci da bana fadar wannan kalma ba.*

.

================

Page 80

 *
 Wajen taron yacika sosai tako Ina ka leqa sojojine sunfii komai yawa awajen yanda kasan kiyashi,
Basu dad'e da isa wajen taron ba, akafara gudanarda taro," *hanna* na gefen MG azaune, alayin manya manyan soldier's, Wanda kowanne zaka Ganshi tareda matarsa agefe, MG ne ya sunkuya dai-dai kunnen *hanna* yace kinsan adahh saidai inzauna nikad'ai kowa gefenshi da matarsa, amma yau kujerata ta k'ara  daraja, tak'ara kima, sai taron yafimun na koyaushe armashi."  Nikaina nasan yanzu nak'ara kima a'idon jama'a,
Murmushi kawai *hanna* tayi amma batace komaiba."
Shima murmushin yayi kawai danya fahimci *hanna* bakowani time ne take bada amsar maganaba, barinma idan maganar tayi mata dad'i sosai."
   Taron yafara ne ga jinjinawa soldier's yadda suke jajircewa, da kwazo, dauriya, saida rayukansu, juriya, they leaves their family, wives, children's, they leaves their home 2save a million lives."  Juyawa *hanna*  tayi ta kalli MG tace always feel proud to have u honey."  I love you😍honey,  love you more cutie😘." Juyadda kanta tayi kawai tana murmushi, shima murmushin yayi yanajin dad'i akoda yaushe, idanta furta idanta furta kalmar so, kuma hakan yabi jinin jikinta yazama kamar ruwan Shanta, akoda yaushe tana cikin furtata."

 

    Haka aka Cigaba da gudanarda taro, dafarko aka fara da soldier's d'inda suka mutu, the worriors, danginsu sun samii kyauta sosai, DA awards Kala-kala sun sadaukarda rayuwarsu, to save other's, da'akazo kan matar shahid sanda su *hanna* sukayi hawaye, itama kanta, tana k'ar6ane tana kuka, shikuwa MG jijjaga Kai kawai yakeyi, Dan jiyakeyi kamar yanzu akayi mutuwar, sosai yakejin zafii cikin ransa,  ya had'a hannayensa waje d'aya ya sunkuyarda kansa kawai yana jijjiga kansa, sanda aka miqa Mata award d'in jikintane yafara rawa takasa k'ar6a, yarontane da baifii 6yrs ba, yasa hannu yak'arba, MG ne yafara Sara masa sannan duk soldiers d'in, sanda suka sarawa yaronnan, danginsa kuwa nawajen, kuka sukeyi Dan yak'ara fama musu ciwon, gashi yaron 1month dasashii a school na  soldier's dake russia, Wanda mahaifinsa yayi, soldiers kenan, sune way'anda dan uwansu zai mutu a ayak'ii sannan kuma wani d'an uwannasa yak'ara shiga."  nan akacigaba da gudanarda taron, kowanne soldier dayaje wannan war, sanda yasamu k'arin girma sosai,"
Wayan *hanna* ne tafara ringing, tana dubawa taga ummii dasaurii tad'auka amma batajii,  toshe kunne d'aya tayi dan hayaniyar wajan bazai barii tajii ba, dukda hakanma bajid'in takeyiba, takalleshi tace honey barinje ummii nakirana kuma banjnta, riqo hannunta yayi yace banson kifita ke kad'ai, mutafii tare, a'a boo kasan fa za'a bukaceka kum,,, shhhhhh yakatseta yace,".  Tashi muje bata k'qrayin musu ba tamiqe,  suka fita tana fita daga hall d'in wani kiran yasake shigowa, picking d'in call din tai sannna, gaisheda ummii tayi cikin, tsintar muryar ummii tayi tana cemata, munkusa isowa wajan taron, Ai *hanna* tsabar murna, bata tsaya Bawa ummii amsaba tajuya tana kallonsa tace, su ummii na hanya sunkusan isowa."  Murmushii  yayi har cikin ransa yajii dad'ii, Tsayuwa sukayi awajan harsanda suka iso, dasaurii *hanna* taje ta, tayi hugging, d'in ummii." Itama ummii hugging back tayi,  sannan tasaketa, cikin nutsuwa, tanufii mai martaba tagaidashi, hark'asa ta tsugunna, shida waziri, harda moddibo, harda labba dasu afeeya, haleema, affan, intisar, sannan kuma mutanen dabatayi zaton ganinsu ummane hameeda, dakuma ya jalal harda Abba, dagudu tayi wajan umma ta rungumeta, tsamm kamar zata shige cikinta, tadad'e ahaka tanjinta kamar ajikin mama take, dakyar tasaketa, tariqe hannunta sannan tace, I love you ummana,  shafo fuskanta tayi tace, love u much more, d'iyata, dahaka tarink'a binsu dai-dai kowa sanda tayi hugging nasa, intisar kam, yatsine fuska tayi itama *hanna* Dan kar ace, Taiwa kowa banda itane, saketa tayi takamo, hameeda, gamm tariqeta tace owhhhh I miss u habibty, tureta hameeda tayi tace," ni da'allah sakenii, sai yanzu kika ganni? Marairaicewa *hanna* tayi tace hava sis, bawani sis several times inakiranki baki d'auka, hmmm *hanna* tace kawai dan batasan amsarda zata bataba, "
MG, Yaya jalal mai martaba waziri, Abba, moddibbo, harsunyii gaba, binsu  abaya suka farayii, hannun *hanna* yana riqeda na labba, suna shiga aka sama musu seat dama tunkafin zuwansu dukda bbu tabbaci amma ansama musu seat, saidai ba'ayi zaton sunkai haka yawa ba, bayan sun zauna ne ya kalli *hanna* wacce dama ita yake jira yace, lokacii yana tafiya, tasowa *hanna* tayi, riqo hannunta yayi suka fara tafiya, k'asada murya tayi tace, boo su ummii fa na kallonmu kasakemun hannu, yiyayi kamar baijiiba, harsuka k'arasa wajan zamansu, itakuwa intisar tacika famm kamar zata fashe, barin yanda taga MG yanuna kamar baita6a kallonta ba, amsa gaisuwarta kawai yayi, sai wani rawarkai yakeyi Allan wannan abar, talura d'azuda hameeda ta tureta har wani d'an razana yayi, tsaki taja wanda yafito fili itakanta bata sqniba, haka akacii gaba da gudanarda taro, kowanni soldier's d'inda sukayii ank'ara musu girma, MG ne kawai yarage, sai ak'arshe aka kirashi Wanda akansa za'a rufe, kallon ,kiransa akayi, kallon *hanna* yayi  yace, ba Good luck kisses ne?" murmusawa tayi tace, aikaima kasan dan cikin mutanene daba saika tambaya ba." But I love you alot alot darling, Dariya kawai yayi yatashi  zuwa wajan." Yanajn sanyii aransa, Yana zuwa ya sarawa wannan babban sojan dake wajan." Wani daga cikin sojojinne yazo ahannunsa d'auke dawani ture, da Jan gyalle, akai d'aukeda golden stamp, soldier din yana tafiya kamar mai yin parade, hannu wansa fararen socks ne qall, yana zuwa gaban MG yaja yatsaya yasara masa shikuma MG yana k'ame, shikuma wannan babban sojan d'aukan abun yayi ,ya mak'alashi agaban aljihun riga MG, yana gama yasasarawa MG, shima MG yasara masa back."
  Alokacin aka nad'a MG yadawo field Marshall, shikansa MG yasha mamaki, Dan bai ta6a d'auka matsayinsa zaikai hakaba." Baiyi zaton zaikai Marshall ba." Bayan angama nad'ashi, parade soldier's d'in dake wajannne, duk shigansu, iri d'aya, da dogayen guns ahannunsu, alokacii d'aya suka d'agata, suka nad'a kunaman, sukayi sama da ita suka sake, sannan suka dawo da ita zuwa kirjnsu suka sauketa k'asa, suka had'e kafofinsu sannan suka Sara.". Cikin takunsa na sojojii yatako, harzuwa gaban mahaifansa ya tsugunna suka saka masa albarka, sannan yajuya zuwaga matarshii,"
Bayan angamane nan akafara gabatarda shagulgula, *hanna* tashi tayi  zuwa tayi gaban matar shahid,takamo hannun yaron Abdallah Wanda yacii sunan MG tace my boy, kamin alk'awarin zakayi karatu, kada ka karaya kamar yanda wasu keyi," muryar matar shahid ne yakatseta, datake cewa, kace bazan yiba harsai kema kinmin alk'awarii zaki haifamun Mata, dariya *hanna* tayi tace har indai matane dasaukii, Allah yakawota zanbaka, but promise me, murmushi yaron kawai yayi alamun ya amince, jawo hannunta tayi tace gasu ummii can harda ummana, k'arasawa sukayi suka gaidasu, nan suka Mata ta'aziya."
Sai magrib kafin aka watse wajan shagalin, gida suka nufa dukansu, 2days kawai zasuyii ,sukoma tareda su *hanna*."
Wanka *hanna* tafayii, sannan shima MG yayi abincii aka shirya, a dining su moddibo maai martaba waziri Abba." Wajansu dabanne, shikuma MG kincii yayi acikinsu yabuk'acii matarsa takai masa nasa d'aki, Dan bai tunanin zai iyacin abincii, batareda itaba."

    _Reader's Ku gafarcenii, najii complain d'inku na mistakes da ake samu, wallhy kwana biyu nadena editing amma yanzu zanrik'ayi Dan jin dad'inku wajan karatu._

To be continued

Ur's

   Z33iiyybawa

*BIBIYATA AKEYI*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

Writing by
     *©zaynab bawa*
*(Z33iiyyb3rw3r)*

_Like my page on Facebook=zaynab  BAWA novels_

 _Join my group on Facebook= ZAYNAB BAWA NOVEL'S_

.
*Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya ce Wanda ya yi sallar nafila rakaa goma sha! biyu tsakanin dare da rana Allah zai gina masa gida a cikin gidan Aljanna.*

*Manzon Allah SAW yace, Wanda ya kiyaye yana yin nafila raka'a hudu kamin sallar azahar da kuma raka'a hudu kamin sallar la'asar to Allah zai haramta masa shiga wuta.*

================

Page 81 

*
  Suna zaune a palour, dasu ummii da umma, gabaki d'aya matan ne azaune awajan, wayan *hanna* tafara ring, tana dubawa kuwa taqa MG ne, dasaurii tayi picking takara akunne," sallama tayi ya amsa, kikawomun abinccii d'aki abunda yafad'a kenan kawai tana shirin yin magana yayi hanging call d'in, cire wayan akunne tayi ta dubii wayan sannan tadubii mutanen wajan,  zamanta tacigaba dayi abunta, yafii 30minute yana jiranta amma shiru, dialing numb d'in ta yayi yak'ara kira, kin recieving  call d'in tayi harya gama ring, wayan hameeda yaso kira amma baida numb d'inta, dialing digit na labba yayi, tana d'auka baijira dogon zance ba yace, ki turomin *hanna*  kawai yakatse kiran, kallon *hanna*  tayi tace antys wai kije injii yaya yareema, shiru *hanna*  tayi kamar batajii taba, kusan 5 minute umma tace wai nii *hanna*  bakijii ana kiranki bane?."    d'an sosa kai tayi sannan tace umma najima yanzu zantashi fa, ok toh tashi kije, miqewa tayi tanufii kitchen, umma ne tace hungo nakii, a kitchen d'in ake kiranki?"   a'a umma abinci fa zand'auko," harara umma ta wurga mata na zakigane ai,"  saurin shigewa kitchen tayi, ummii najinsu banda murnushi bbu abunda takeyi, ita harcikin ranta tajii da d'in yadda taga Suna zaune lpy, gashi dukansu sunyii k'iba sunyii kyau."
  Kitchen d'in takarsa, Had'a abincin tayi waje d'aya,  tad'aukoshi atire tafara tafiya tanufii stairs, azuciyarta tana cewa inbanda fitina wai aceh sai mutum yahau samada abincii, ahaka tak'arasa har k'ofan d'akin tana gungunii, sa k'afa tayi ta bugii k'ofan yanda zaijii yazo yabud'e, baifii 3sec ba yazo yabud'e wanda dama kamar jiranta yakeyi abakin k'ofan, juyawa yayi yakoma bayan yabud'e,  haushine yacikata wato idan taga dama ta ajiye koh," kwala masa kira tayii, heyy mashall, juyowa yayi yace yess cutie, nuna masa tire na hannunta tayi da ido bbu musu yazo yak'arba, juyawa tayi, yayi saurin ajiyewa ya kamota, d'aukanta yayi cakk yasa kafansa ya rufee k'ofan sanda yakaita gaban tire d'in kafin yasauk'eta, serve me yace, bbu musu ta zaune tafara zuba masa, tana gamawa tamiqa masa plate d'in, girgiza kai yayi yace feed me, dafa goshinta tayi🤦‍♀ tace, owwh honey kafiya rigima kamar k'aramin yaro," oyah feed me, yak'ara cewa, bbu musu tad'auki plate a cinyanta tafara feeding nasa," ci yayi sanda yakoshi ta dubeshi tace, u knw wat darling?" girgiza kai yayi yace nop saikin fad'a, I LOVE U,  lumshe idanuwa kawai yayi yanajn sunyii ci kin ransa."  cikin apple data yayanka tana shirin miqa mata, tad'auki d'aya tasaka abakinta tana cewa yau 5month currr da aurenmu, bud'e ido yayi yak'ura matasu, ganin  irin kallon da yake mata yasata cewa meneh?" bud'e baki yayi yace, tunanii nakeyi kamar bake bane da bakiso ne, bakison aurenaba, harara ta wurga masa ta tamke rai kamar bata ta6ayiin dariya ba tace, kagafa banso kabarii, kama kunnuwansa yayi yace nabari dear afuwan, fuskantan baisakeba tana kahmaa sake d'in mana, bazanma sake d'inba yafad'a."  yau muncika 5month ko?" uhumm ta fad'a tana tura apple abakinta,  tsayawa yayi yace, wai nii apple d'innan mani kike yankawa koma kankii, ohow 💁 taba shi amsa, jijjiga kai kawai yayi yamiqe yana cewa tashi inkaiki shan ice cream toh for 5 month, dasaurinta tamiqe tafara shirin tafiya."
Farin material tasaka, qal har d'aukan idanu yakeyi, sannan ta d'auka gyalenta baki kirin tasa, dakuma bak'iin flat shoe." shima Farin yadii ya saka mai aikin bak'ii, sannan da bak'iin links, bak'iin takalmi, da hula bak'a, sunyiii masifar kyau idan kagansu,"
kansu fita sanda *hanna* tamusu selfie, fesa turare yakeyi tamiqa masa hannu alamun yabata, girgiza kai yayi yace wannan turaren yayi k'arfii za'ayita kallonki fa, zaija hankalin mutane, turo baki tayi tace, to ai dakai zanyii tafiyan, idan aka kalleni saika hararesu, k'in bata yayi tayi narai-narai da ido kamar mai shirin yin kuka."  miqa mata yayi da saurii, tasake fuska takar6a," murmushi yayi yana kallonta, tana fesawa yak'ura mata ido yace, cutie naga alamun kindawo drama queen, kaman asmy d'in AJ."  dariya tayi tace nidai dear, asmy tafini rikicii, fara gaba yayi yace toh najii, mutafii time is going, futowa tayi harsun fara jerawa tayi saurin yin gaba, dan kadasu ummii sugansu haknne yasa tawuce gaba." hakan kuwa bak'aramin kyau yayiba."  gabaki d'aya sai suka d'auki hankalin mutannen palour d'in dan bak'aramin kyau sukayiba."
 Kuma sundace da juna, sosai da cewar su tafito, sauk'a sukayi har zuwa gabansu, d'an sosa kai yayi sannan yace, uhmmmm bari mud'an fita, murmushi ummii tayi tace saikun dawo, Itama umma murmushin kawai tayi, sai mundawo *hanna* tace sannan tajuya suka nufiii hanya, muryar labba ne tatsayarda ita cawe, plz antys asiyo mana ice cream, toh dear kawai *hanna* tace, harta juya, muryar intisar takatsesu da cewa, kujirani, am bored here, Zaman ya gundu renii, juyawa *hanna* ranta abace lallai yarinyarnan y'ar rainin hankaline," itama ummii  har ranta batajii da d'in yanda intisar ta nuna zata bisu ba, dan hakan shiga hakk'ii ne, amma bazatayi maganaba, dan batason rikicii yanzu saita fad'awa kilishii kan anmata wulakancii." 6atarai MG yayi yace, baki kallon y'an uwanki azaune agidane, uhmmmm su daban ai, nidai nagajii, yabud'e baki zaik'arayin magana *hanna* tayi saurin riqo hannunsa, juyawa yayi ya kalleta, girgiza masa kai tayi, sannan tajuya ta kalli intisar tace kizo mutafii, yatsina fuska tayi ta surii gyalenta, juyawa  yayi yakalli, hameeda yace ku taso mutafii, wani bak'iin cikine yatokare intisar amma dai dukda hakan aita hanasu jin dad'ii."  tashi sukayi suka d'auki mayafinsu, labba ma cike da haushin intisar, kwata-kwata abunda tayi bata kyautaba, tasan kowaye aka masa hakan bawai dad'ii zaijii ba."
  marshall ne yafara futa, itakuma *hanna* tatsaya jiransu su fita tare, atsaye taga, marshall abakin wata black car, mai tinted bak'ii wulik."   k'arasawa tayi gabansa tace munfitoo, kuzo mutafii, yace, labba ne tayi saurin katse zancen da cewa yaa yareema, dama kasa d'aya daga cikin soldier's dinka yajamuu,  sai mubiku abaya."
Murmushin jin dad'in shawararta yayi yace, allrt habibty barina masa magana, harara  intisar tawatsawa labba, itakuwa labba ta d'auke kai kamar bataganii ba."
  Dawoawa yayi yanuna musu motar yace, kuje cann ga motarnan, hameeda da labba ne suka nufii motar suna tad'insu, itakuwa intisar tsayawa tayi ba abun tace takoma ba."  haushi duk yacikata."
Juyawa tayi cikin bak'iin ciki ta nufii d'aya motan."
Wani soldier ne yazo da niyyar kar6an key na motan, marshall ya tsayardashi,  yace shi zaiyii driving da kansa, bbu musu yaja baya, shikuma ya bud'ewa *hanna* k'ofa sanda ta shiga tazauna sannan ya zagaya driver seat aka bud'e masa ya shiga yazauna.", d'aukan hanyan sukayi, dukda bashi kad'ai bane da soldier's amma ratansu baiyi kusada kusaba."
  Yana driving d'aya hannunsa, Yana cikin na *hanna*." Yana driving ahankali suna shan hiransu abun gwanin ban sha'awa😍."
  intisar a motan banda tsaki bbu abunda takeyii, ganin tacikasu suka fara tad'ii. suna shewa."

Wani k'aton mall suka nufa, bayan sun isa, yad'auki wayansa yakira soldier d'in da kejan motan su yace masa yashigarda su, duk abunda sukeso su saya." Yana ajiye wayar yajuya ya kalli *hanna* wanda itama shi d'in take kallo yace, cutiee piee, yes honeyy boo," jibi zamu koma gida, jijjaga kai tayi sannan tace inadai baka manta alqawarinda kamun ba?, ban mantaba, dear amma ai maman ma zatazo, dan za'ayi walima najii mai martaba Yana fad'ii."  komadai menene idan tazo zanbita naje muyii satii, zaro ido yayi yace satii dai cutiee? eh satii, gaskiya bazan iya barinkii kiyii satii ba, hmmm kawai tace, bata k'ara cewa komaiba, aranta tana cewa idan na tafii basaiga ganni ba."  kinsan me ya tambayeta, a'a ta bashi amsa, bilal fa yafad'amun yatura iyayensa sun tambaya masa, 6ta dinki hafsat kuma anbashi, yanzu haka dai saura biki,"  dariya tayi tace ai nidai naga alamu tun bikinmu amma tace ba haka ba, shima dariyan yayi yace yanzu ai batada bakin musu."
 Shiru sukayi na y'an seconds, kwantarda kanta kafad'unsa tayi tace, kasan mene?"  a'a dear saikin fad'a, inason hameeda ta aurii captain Ahmad, lumhse idanuwa yayi yace, in sha Allah, zancika miki burinkii."  Shiru tasakeyi tace dear, yafii 2minute kafin yace, uhumm, yanzu idan babuni zaka manta dani sannan ka sake aureko? D'agowa yayi yadubeta yace, wani irin zance kikeyi haka? Kawai jinakeyi kamar wata rana zamu zama seprated, kwananna wasu irin mafarkai nakeyi, ganii nakeyi kamar zanmutu inbarka, ganii nakeyi kamar rayuwata ta gaba da zanyii dakai batada nis,,,  daka mata wata rikicecciyar tsawa yayi wanda har jikinta sanda yafara rawa yace shutupp, shutupp, baki da hankaline, kinfara ta6uwa ne zakina mun irin wannan zancen."  harwani hucii yakeyi, hannu takai zata ta6ashi yayi saurin bige hannunta, yabud'e yafice, idanuwantane yaciko da hawaye, ita kanta batasn maiyake damunta ba." goge hawayen tayi itama tafuce, cann nesa ta hangoshi, da gudu taje tayi hugging back d'insa." dasaurii yajuyo shima yayi hugging d'inta tight, yafara magana cikin tashin hankali yace, plz kada kisake mun irin wannan maganar Yana d'agamun hankali, gabaki d'aya yasa jikina yayi sanyii."  kada ki kara, kwantarda kanta tayi aqirjinsa dai-dai saitin zuciyarsa, tanajii yanda zuciyarsa ke bugawa da k'arfii ga saurii." D'agowa tayi tace nabarii kayafenii, dan Allah zuciyarka tadaina bugawa da k'arfii haka."  kidena tsoratata idan bakiso ta bugada k'arfii, nadaina wallhy nadaina."
Zama yayi awajen itama tabishi tazauna ta kwantarda kanta akafad'ansa," iskane mai dad'ii take kad'awa awajen, lumhse idanuwanta tayi, shikuma ya nata tunani, har yanzu zuciyarsa tasaka cire zullumin abunda *hanna* ta fad'a masa." lumhse idanuwa yayi yace cutie, uhum ta amsa alamun bacci yanason kamata." baza kisha ice cream d'in bane?"  zansha mana, to ai naga bacci kikejii."  kacewa hameeda tasiya mun idan muka koma saina k'ar6a."  wayanta yak'ar6a yakira hameeda yace ta siya mata ice cream."  Ganin bacci yacii k'arfinta yasa yad'auketa cakk yayi mota da ita."
  Suna zuwa dai-dai mota saigasu sunfito, kallon takaicii intisar tamusu ta ebesu tawatsar."  aranta ta kudurta, sai ta rabasu dan bazata jurii Ganin  abun takaicii ba."
  Sakata aback seat na motan yayi sannan ya miqawa, wani soldier car key, yashiga yakwantarda kanta acinyansa."
Har suka k'arasa gidan Suna haka lokacin baccinta yayi nauyii, d'aukanta yak'arayi yafito da ita, yadubii hameeda yace ki sakamata afrigde,  yana fad'in haka yawuce, sama yahau da ita, kwantarda ita yayi sannan shima ya kwanta dan dare yayi."
  Washe gari da sassafe suka shirya suka nufii get together da soldier's suka had'a, basu suka dawo ba sai dabb magrib, sallah sukayi sannan, suka cii abincii, sai alokacin *hanna* tasamu suka zauna itada yaya jalal, tad'ii sukayii sosai yana bata labarin amira tanashan dariya."  sai dare sosai tukunna *hanna* tatashi tayiwa yaya jalal sallama, har ta juyawa, tajuyo takalli yaya jalal, tace yaya jalal ni bakaga wani canjii daga garenii ba?."  dariya yayi yace kinyi kyau mana kanwata, girgiza kai tayi tace yaya bahaka nake nufii ba,  ba ka kallon yanayina ya canja, kallonta yayi yasake yace nikam banga komai ba, meya fari?"  yaya haka kawai nakejina kaman baniba, wani lokacin sai injii kamar inzauna inyitayin kuka, kokuma inshiga duniya." subhanalhi me kike fad'ii haka *hanna* wallhy nima yaya bansaniba kwata-kwata bansan abunda yake damuna ba."  kinfad'awa umma ko masa?"  A'a banfad'a ba yaya dan Allah kaima karka gayamusu banso hankalin su ya tashi, bazan fad'a ba amma kirink'a yin addu'a to yaya ta fad'a sannan tajuya."
Marshall dake saukowa jin irin maganrda *hanna* tajeyi yasashi tsayawa, ga baki d'aya jikinsa yayi sunyiii, baisan maiyake damun *hanna* ba?" juyawa shima yayi yafasa abunda zaiyii ya juyawa yakoma, kwanciya yayi yabawa k'ofa baya, itama shigowa tayi ta kwanta gefensa, kiran sunansa tayi jin bai amsa ba yasa ta d'auka yana baccine, kashe bedshide lamp tayi tamatso kusadashi tayi hugging back d'insa, runtse idanuwa yayi yanajin, sonta cikin ransa, ahaka bacci yayi gaba da ita, shikuma duk satan barcii haka yaganshi yabarshi."

Washe garii da sassafe flight d'insa yatashi, zuwa NIGERIA."

  _Safe flight marshall and *hanna*_

To be continued

Ur's
    Z33iiyyb3rw3r


. *BIBIYATA AKEYI*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

Writing by
     *©zaynab bawa*
*(Z33iiyyb3rw3r)*

_Like my page on Facebook=zaynab  BAWA novels_

 _Join my group on Facebook= ZAYNAB BAWA NOVEL'S_

  .
```Manzon Allah SAW Yana cewa," Wanda ya yi alwala, bayan ya kare alwala sai ya ce Ash-hadu alla ilAha illallAh wahadahu lasharika lahu wa anna muhammadan Abduhu wara suluhu. Allahumma Ja'alni minattauwabina waja'alni minal mutadhahhirina.
Duk wanda ya fadi wannan bayan gama Alwalar sa to za'a bude masa kofofin Aljanna guda takwas ya zabi wadda ya ke son shiga.```


```Manzon Allah SAW Yana cewa,"  Wanda ya yi alwala bayan ya kammala alwalar sa kaf, sai ya ce Subhanakallahumma Wabihamdika ash  -hadu allah Ilaha illallah anta astagfiruka wa'atubu ilaika.
Zaa rubuta wannan acikin wata takarda baza'a bude ta ba sai ranar lahira ya ga alkhairin da ke cikin ta.```

================

   *wayyo Allah cikina😂😂😂😂 u guys are funny, BIBIYATA AKEYI FANS, WALLHY kunyi arayuwa, ranar nacii dariya Allah, Ina la6e Ina kallaonku, masu kuka yanzu kuka fara fa tamm🤷‍♀ Danni Dai bbu ruwana."😬😛  saidai kada acikamin group da hawaye."😭 Hawwer😘 darling wato hadda ke ay'an kuka nidai bzan hanaku ba🤷‍♀ bbu ruwana." _~ILYSM~_* ```INASONKU HAR CIKIN RAINA```😍❤

================

 page  82

  *
    Cikin jirgii *hanna* nazaune kusada Marshall, ta kwantarda kanta akafad'ansa, tayi shiru alamun wani abun take tunanii."
Shikuma marshall yak'ura mata idanuwa kawai ganin yanda tayi nisa Cikin tunani."
Wata doguwar ajiyar zuciya tasauk'e, sannan ta lumhse idanuwanta, kallonta yakeyi ko kiftawa bbu, itakuma bata dad'e da rufe idanuwa ba bacci yad'auketa."
  Shima runtse idanuwansa yayi Cikin zuciyarsa yana addu'a ya Allah kada ka jarabceni da abunda bazan iyaba,  ya Allah kada ka nunamin ranarda zan rasa *hanna* arayuwata, bansan wani halii zai shiga ba." Ahaka har jirginsu yayi landing *hanna* tana bacci, baisan katseta daga baccinta data lula kuma alamun baccin yana mata dad'ii, hakanne yasa ya cewa su ummii su fara gaba, shi zai k'araso daga baya, akawai abunda zaiyine, su ummiii way'anda sukazo taryansu daga fadah sukabii," shikuma yazauna jiran *hanna*, ga mutane dayawa dasuka zo taryansa, kama daga shugaban k'asa governor's, ambasador's ministers, Senate, dasauran su."
Tafii 30 minute tana bacci,  wata ajiyar zuciya tasaki, sannan tayi miqa   ta had'a da addu'an farkawa daga bacci, ware idanuwanta tafarayi, akansa ta ware idanuwannata tass, murmushi yasakar mata, itama murmushin tamayar masa,"  juyawa tayi da niyyar ganin su umma amma taga wayam dasauri tamiqe tazauna, zaro ido tayi tace ina ummii suke?"
Suntafii gida."  zaro ido tayi tace toh mu me muka tsaya yi?."  kajimun yarinya, me kike tunanin natsaya yii, kozan tasheki a bacci ne?" ehem, common tashi mutafii."  marairaice fuska tayi tace yi hak'uri dear, aida ka tasheni."  intasheki kuma?."  A'a kam gaskiya bazan iyaba."  yanzu kawai tashi muje, nasan ana jirana."  miqewa tayi tada'uko gyalenta ta yafa."   ya riqo hannunta suka futa."    ana bud'e door na flight d'in, flashes ne suka fara kashe musu ido, sa hannu *hanna* tayi ta k'are fuskanta, saida tad'an dad'e kafin tabud'e fuskan."  sojojine atsaye bakin jet d'in, alamu ya nuna sundad'e a tsaye awajen,"  suna sauk'owa mutanen da sukazo taryansu, suma suka k'arasaso, hannu suka fara bashi kowannen su wasu na haugging d'in sa."  amma dukda haka hannunsa yana cikin na *hanna* gam yariqeta, dan yasan *hanna* yanzu saita rikice batason hayaniya sosai, barin yanda yalurada ita kwana kinnan."
  Ahaka har suka rakashi zuwa ga mota, duk yanda y'an jarida sukaso zantawa dashi bai tsayaaba, damuwarsa yakai *hanna* gida ta huta, dakansa ya bud'e wa *hanna* Mota tashiga yayinda mutanen wajan tsan-tsan mamaki ya tsaresu, lallai sun tabbatr duk Mulkin mutum sayya sauk'arda Kai a wajan mace, bud'e masa motan akayi   sai shima ya shiga, haka suka tafii gayya guda zuwa fadah."
 Bayan sun isa ne aka bud'e k'ofan *hanna* tayi saurin fita tanufii shashin ummii."   su kuma dasauran jama'a aka wuce cikin fadah."
  A palour tasamu su ummii nan ta shiga tayi sallololinta tafito, tasamu abinciii tacii sannan tazauna A palour tarashe."
  Data gajii da zaman ne tashige d'akin labba takwanta dan batajin dad'in jikinta."  bacci tayi sosai sai Bayan sallan magrib tatashi."  tayi sallan ta sannan tak'ara dawowa palourn tasamii ummii, su afeeya sun tafii."
Har kusan k'arfe 9 tana wajan ummii, sai lokacin marshall yazo suka wuce shashin su, komai agyare suka sameshi."  saboda gajiya wanka kawai sukayi sannan suka kwanta."
 Washe gari kuwa agida suka yini bawanda yafita, dan sun dad'e basu samii hutu irin hakaba."
 Suna zaune afalo hanna tad'aura k'afofinta kan cinyan marshall tana danne danne awayanta,"  kallonta marshall yayi ya maido duk hamkalinsa gareta, yace, cutie, uhmm ta amsa, yakamata kije kingaida umma (kilishi) yau,"  kinsan gobe bbu lokacii kina wajan zancen walimah, bata d'ago ta kalleshi ba tace, zuwa jimawa zanje."  tom kawai yace yacigaba da kallonsa dayakeyi."

  K'arfe takwas dai-dai *hanna* ta zumbula hijabinta tanufii shashin kilishii koda taje a palour tasameta, da fara'a, kilishii ta k'ar6eta sai riritata takeyii, itakuwa *hanna* taji dad'in hakan, kilishii ne tayi wata y'ar dariyar da kana kallonta kasan ta munafurcii ne tace, y'ata nashiga tashin hankali sosai, lokacin tafiyarsu yareema, gashi kuma kema kika shiga wani hali, ga baki d'aya hankalin mu atashe yake, mungaza sukunii, sunkuyarda kanta *hanna* tayi tace, ai gashi mundawo umma yanzu hankalin ku zai kwanta, wata dariyar kilishii tak'arayi tace ai kuwa y'arnan, yanzu munjii sanyii sosai." aff kinga na sha'afah tun d'azu nahad'a miki zobo akan zan aika miki tunda kinzo aisai ki tafii dashi tafad'a tana miqewa, wani irin kwad'ayine yazowa *hanna* gabaki d'aya yawunta ya tsinke, Allah Allah takeyi akawo zo6on tasamu tasha, Har wani had'iye miyau takeyii."
  Da k'aton jug kilishii tadawo riqe ahannunta, ajiyewa tayi agaban *hanna*, cikin kunya *hanna* tace umma a'iina zan samu cup, inaso nasha ne," dasaurii kilishii takwala wa wata kuyanga kira, umarnii tamata data d'auko cup, bata dad'e ba kuwa tadawo hannunta riqeda cup, ajiyewa tayi agaban *hanna* sannan tanemi izini ta zuba mata, k'ar6a *hanna* tayi takafa bakin ta tahausha zuciyarta d'aya, sanda tashanye sannan tatshi zata fita, umarnii kilishii tayi da a d'auki jug d'in abita dashi, godiya tayi sosai sannan tafice."
Wata dariyar rainin hankali kilishii tayi tacce lallai wannan yarinya, shsshasha ce, kokad'an batasan mai sonta ba, inbanda abinki niceh zan miki zo6on? toko shi mijinnaki baikai wannan matsayinba, taja tsaki."
Itakuwa *hanna* tana komawa sashenta, da kad'an kad'an taringa shan zo6on harta shanye tass, dan wani irin kwadayin zo6onne yakamata."
  Sanda tashanye kafin ta tuno bata ragewa Marshall ba, d'aga kafad'unta tayi🤷‍♀, sannan tace ohow, idan yazo zangaya masa." dan tunda yafita d'azu haryanzu bataga idanuwansa ba, shirye shirye bikkunan da za'ayi yasa Marshall baidawo gidaba Sai kusan 10:15pm."  *hanna* na jiransa afalo dan yakanyii wuya ta iya bacci idan baikusada ita shiyasa take jiransa Yadawo."  da sallama yashigo ta amsa masa tana murmushi, yana zuwa ya zauna kusada ita."
Sannu da dawowa yauwa cutie ya gidan?"  Lafiya klau, ya ayyukan? klau cutie na, gaskiya yakamata abarmunkai ka huta haka, uhmm ainakusa fara hutuna, sai nayi months banfita ko nan da door ba, dariya *hanna* tayi sannan tace," kahuta Sai kayi wanka naga Kamar agajiye kake, kaman kinsani nagaji dayawa."  yafii 30minute akwance a cinyanta, idanuwansa alumshe, amma Kuma ba bacci yakeyii ba." *hanna* na wasa da gashin giransa dake had'e waje d'aya, bud'e idanuwansa yayi yace dear nagama hutun zanyi wanka." ok tom tashi muje."
 Bayan yafito awankane Har yayi shirin kwanciya, *hanna* ta dubeshi, afff namanta honey, naje nagaida umma,  harta bani zo6o."  gaban Marshall ne yayi mugun fad'uwa Jin ta ambacii zo6o,  shikqnsa baisan dalilin fad'uwar gabanba."  shiru yayi baice komaiba, Sai Bayan *hanna* takwanta Har bacci nashirin ebanta, cutie yakira sunanata, uhmm ta amsa alamun bacci yafara kamata."  kinsha zo6onne?"
Uhmm nasha kayi hak'urii ban bar makaba amma gobe zanyi mana wani." I LOVE YOU, yafad'a tana k'ara gyara kwanciyarta, uhmm kawaii yace baik'arayin maganaba." 
Kusan 3 nadare hanna ke kwance tana baccinta,
Shikuma Marshall Yana sallah, dan tunda *hanna* tafara way'annan irin abubuwan, bai iya bacci."
Bayan ya idarda sallan yazauna Yana addu'oii wani irin ihuu *hanna* takwala, tatashi tana ihuu tana riqe kanta,  tana cewa honey zasu kashenii, gasuncan, wayyo Allah tak'ara sake wani ihunn, tana shirin sauk'a daga gadon, da gudu Marshall yayi kanta."

To be continued

Ur's

      z33iiyybawa

*BIBIYATA AKEYI*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

Writing by
     *©zaynab bawa*
*(Z33iiyyb3rw3r)*

_Like my page on Facebook=zaynab  BAWA novels_

 _Join my group on Facebook= ZAYNAB BAWA NOVEL'S_

```Wani sahabi yace, rana mun kasance muna Sallah a bayan Manzon Allah (S.A.W) da Annabi ya dakko daga ruku'u sai ya ce Sami'Allahu Liman Hamidahu sai wani mutum daga cikin sahabbai yace Rabbana Walakal Hamdu, Handan Kasiran Dayyiban Mubarakan Fihi da aka gama sai Manzon Allah ya waiwayo sai ya ce Wanene ya fadi wannan sai mutumin yace Ni ne ya Manzon Allah sai Manzon Allah ya ce Naga Malaika talatin da "yan kai suna rigagato wazai rubuta wannan aiki yaje ya gayawa Allah.```

 .
================

Page 83
*

  Riqeta yayi, tayin saurin shigewa jikinsa tana kuka tanacewa Wallhy zasu kamanii."
  Shhhhh yasa hannu abakinta dear bbu wanda xai kamaki."  kiyi shiru."
Shirun tayi tana ajiyar zuciya addu'oii yaringa tofamata Amma duk da haka tak'i sakeshi, Kuma tak'yin bacci."
Kiran sallah ne yasashi yatashi yanufii band'aki kank'ameshi tayi tace Ina zakaje?" toilet zanyii alwala ankira sallah."  girgiza Kai tayi Kamar mai shirin yin kuka tace dan Allah kayi sallah anan kada kafita, murnusawa yayi sannan yace tom dear taso muje muyi alwala, tare kuwa sukayi dan ko nan dacan bataso yamatsa, bayan sun idarda sallan ne yace cutie jeki kwanta nizan futa."
Girgiza masa Kai tayi hawaye na shirin zuba, matsowa kuasada ita yayi yace ya rabb, bazan fitaba maza wipe ur tear's, bbu musu ta goge hawayan," Jan hannunta yayi yakwantarda ita Shima yakwanta kuasada ita." addu'a yayi ta mata Har tayi bacci."  Sanda yaga baccin nata yayi nisa ne, yazare jikinsa yafice, dan biki za'ayii a government house, na murnar cigabanda k'asar tasamu na marshall."  7:00.am dai-dai, *hanna* taji Ana tashinta, cutie, cutie, uhummm ta amsa cikin muryar Mai bacci, tashi maza, bak'i zasu fara zuwa baki shiryaba." toh tace tana k'okarin miqewa, tashi tayi tazauna tana murmurza idanuwanta."  cikin shagwa6a tace wallhy ni hone,,,,,,,,  saurin yin shiru tayi ganin yadda ta bud'e idanuwa bataga komaiba."  wani tsorone ya ziyarcii zuciyarta."  tashi tayi jikinta Yana 6ari tayi bandaki, Kai tsaye bud'ewa tayi kozataganshi, nanma Wayan Kuma batajii bud'e k'ofa ba."  suran wayanta tayi tafuta, abakin k'ofa tatsaya tatambayi wani soldier nan yashaida mata ai tun asuba yafita, bata iya komawa cikin gidanba, Kiran labba tayi tace, habibty dan Allah kizo yanzu kitayani zama, toh labba tace sannan takashe Wayan."
  Kiran hameeda tayi nan ma tace da'allah tazo."   jiran labba tayi Sanda tak'araso sannan suga shiga tare."
  Tad'ii suka zauna yii, ba'adade ba kuwa saiga hameeda nan tashigo itada hafsat, dagudu ta rungume hafsat tana murnar ganinta."
  Sunfii 15 minute suna hira kafin *hanna* taji muryar ammah, aikuwa da gudu tatashi tayi Kan Amma, itama Amma murnar ganinta takeyii."  sauk'a sosai *hanna* tamata Har tarasa mame zata kawo mata."  Ammah batafii 20 minute ba tatashi tace Jalal na jiranta amota."  kuka *hanna* tasaka tana cewa haba Ammah na, wata na nawa bangan Kiba? Da kina zuwa zakice Zaki tafii."
  Jawota Ammah tayi tana fad'in haba d'iyata, kibar kuka, zuwa jimawa zandawo dakyar ta lallasheta tayi shiru."
K'arfe 4 dai-dai akafara walima, zuwa 6 aka gama, mama batazoba, saboda su karima."
  *Hanna* sashinta tawuce, bayan angama,  tayi sallah ne tashiga kitchen, tafara had'a masa abincii, bata d'auki lokacii ba tagama dan dama bawani Mai nauyii bane."
  D'aki tashiga tayi sallan isha, tafito tashiga kitchen dan dawoda abincin dining."  da k'arfii ta ji muryar Marshall Yana cewa cutieee, itama da k'arfin ta amsa, yess honey, am home, ok boo am coming tafad'a tana wanke hannuwanta tafito."
Wayam tagani babu kowa afalon da k'arfiii tace honey where are you?" Jin shiru yasata shiga d'ayan falon nanma shiru babu kowa, Kuma da'alamu ba'a bud'e k'ofaba."
  Komawa tayi nan danan jikinta yad'auki rawa, kudin dinewa tayi Akan Kujera, sai Kusan 11:30 taji k'arar bud'e k'ofa lokacin tayi kuka harta gaji, abubuwan dataji a wannan lokacii naban tsoro baya fad'uwa."  Jin bud'e k'ofa tayi saurin juyawa."  ganin Marshall dasaurii tak'arasa da gudu ta rungumoshi, tana cewa honey kafita dani daga gidannan, wallhy akwai aljanu aciki nibazan iya zamaba."  kuka takeyii Kamar ranta zai futa."
Rungume ta yayi sosai Yana rattshinta, Amma *hanna* ta birkice masa, bayanda baiyiba daga baya Kuma tafara ihuu Kamar wata mai aljanu."
Da k'arfinsa yariqota ya rungume tsam ajikinsa."  bayadda batayi ta kwace kanta ba, Amma takasa, dan ko jijjiga bayayi."  Sanda yaga tadaina muzul muzul yad'agota, idanuwansa sunyii jawur, yarasa maiyake damun *hanna*, yarasa tayadda zai shawo Kan matsalarta."
 Ido ya k'ura mata ganin yanda take sauk'e ajiyar zuciya."
 K'ara maida ita jikinsa yayi, ganin bacci yad'auketa yasashi tashi da ita yanufii Sama, kwantarda ita yayi sannan Shima yawanta agefenta, Sanda yakai 2hours kafin yatashi yad'auro alwala, yafara nafila."
Bashi yatashi daga sallaya ba, saida yauma Kamar jiya, da ihun *hanna*, yaukam Har Gari yawaye bbu wanda ya k'ara rintsawa acikinsu."
Gari na wayewa Kuma wani irin bacci yad'auketa,"
Sai 12 tafarka,"
Marshall yab'oye damuwarsa kwataa kwataa yakii gayawa ummii maiyake faruwa, dan gani yakeyi Kamar zaishawo Kan matsalar."
 Ahaka ya wunii bbu yanda yajeshi Yana tareda *hanna* itama bataso yafitan dan haka yazauna."
  Saida 9 nadare yayi  suna zaune akujera, sallamar intisar ce ta ziyarcii kunnuwansu."
Amsawa sukayi ta shigo tazauna, gaisheda Marshall tayi tazauna, sannan ayatsine tadubii *hanna* tace sannuu, *hanna* Kuma ko kallonta batayiba. Balle tasan tanayii."
Miqewa Marshall yayi yace yawwa tunda ga intisarnan barina shiga wajan ummii na nemo Miki kindirmon kijiranii yanzu zandawo."  to kawaii tace yamata peck a forehead ya fice."  haryad'an fara tafiya yatuno bai tambayeta da yamrii takeso kokuma furaba, juyawa yayi  yakoma palour d'in."  muryar intisar ce takatseshi daga magarnarda yake shirin yii, tana cewa aike banza ce tunda nafad'a miki Saina rabaki dashi Kuma baki hannani kusantar yanda yakeba."  idon Marshall harwani k'ankancewa sukeyi tsabar 6acin rai, idanda kalmar daya tsana arayuwarsa bai wuce a ambacii rabuwa tsakaninsa da *hanna* ba."   cii gaba tayi dacewa, Kuma nayi rantsuwa bazanyi kaffara ba, sai kin d'andani rashinsa akusadake."  *hanna* wacce kwataa kwataa batason hayaniya ta lumshe idanuwanta ko tanka mata batayiba."
 Wata tsawa Marshall yadaka mata wacce ba ita d'aya ba Har *hanna* Sanda tarazana, Yana k'arasowa wajan yad'auketa da marii, bata ankara ba yak'ara mata wani."
Saida tafad'ii Kan kujera yanunata da yatsa yace fucemin, fucemin nace tun kafin na tattaka ki."  da gudu tafice tana kallon tara-tara wani ikon Allah ne kawaii yakawota sashin kilishi, Jin kukanta kilishi tafito da gudu, ganin fuskar intisar akumbure, Maiya sameki? tafara tambaya, cikin kuka intisar tafad'a mata abunda yafaru." Wata ashar kilishi ta lailayo tasake, dan kaza kazansa Akan wannan matar tasa zaimiki haka to wallhy nayi rantsuwa saina rabasu, saita fara haukar Tata da gaske, yanzu bakad'an takeyiba?"
To wallhy saitayi haukan gaske."  Kuma aure Kamar kin aureshi angama tafad'a tana surar wayarta tayi ciki."

To be continued

Ur's

     Z33iiyyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

Writing by
     *©zaynab bawa*
*(Z33iiyyb3rw3r)*

_Like my page on Facebook=zaynab  BAWA novels_

 _Join my group on Facebook= ZAYNAB BAWA NOVEL'S_

*Inna lillahi wa'inna ilaihi raji'un, plz ur prayer's are needed, yarinyar 6tana ta karye ak'afa😭😭😭 wallhy har cikin jikina nakejii, dan Allah ku mata addu'a."*

================

   *Weldone dear, kinyi namijin kok'arii, a littafinki na BAYAN AUREN💑 , Allah yataimaka, yakara kaifin basira, muna jiranki alittafinki nagaba."  jinjina gareki."*

.

================

Page  84

*
   K'arasawa kusada ita yayi yazauna, yace cutie kiyi hak'uri kinjii?"  am srry, jijjiga kai tayi sannan tace bbu komai tak'ara komawa ta lafe akan kujeran."
  Haka yakasa futa dan tunaninsa d'aya, wani hali zata shiga idanya barta." 

  kilishii ce zaune a bedroom dinta, waya takeyi tana cewa, wallhy nagajii da wannan yarinyar, duk abubwan da nakeyi amma abuu yacii tura, shawararki ta farkon kawai zanbii."  yanzu ki kirashi basai safiya ba, ahaukatarda ita, shiru tayi na y'an wasu dakikai sannan tace, to ai yanzu nagane, yanzu abunda nakeso kawai zuwa safiya, nafarka najii, ance tahaukace,"  zuwa safiya zanturo miki da kud'in."
Kashe wayar tayi tana hucii."


  Da daddare kuwa marshall ganin yanda jikin *hanna* yayi zafii zazza6i yarufeta, baisamu daman yin sallah ba."  kwana tayi ajikinsa tana kyarma, shikuma yana riqeda ita haka bai iya runtsawa ba."
 Da asuba dakyar yasamu ya kwaci jikinsa yayi sallah itakuma *hanna* ko sallah bata iya tashi tayiba."
 Kusan 7 yasauk'a kitchen yahad'a mata tea mai kaurii, yahau sama, duk yanda yaso *hanna* ta sha tak'ii, dan bakintama rawa yakeyi."   har 9:00.am *hanna* bata bud'e idanuwanta ba, zuwa wannan lokaci iya tashin hankali marshall ya shigeshi."
Idanuwansa sunyiii jazirr, kamar qauta, hawayene kawai bai zuba a idanuwansa ba." hakanma dan yakasance mai taurin zuciya ne shine yahanashi zubda hawaye." 
Sai 10:00.am kafin *hanna*  tatashi, sai yazamana kamar ancire mata ciwon."
Riqo hannunta yayi yace, yawwa cutie tunda kintashi, muje kisa wani abuu bakinki."  yatsine fuska tayi tace banfa yi sallah ba."  ok tom sha tea d'in da ke gabanki tukunna, ai lapiyanki klau baki fashin sallah, lalurine ko dear, gyada masa kai tayi, yad'auko cup d'in yana shirin kaiwa bakinta, wani irin juyawa kanta yafarayii, dafe kanta tayi saikuma tasake, tatsaya tana kallon sa."  kaiwa cup d'in bakinta yayi ta saka hannu ta bige cup d'in ya watse ajikinsa." kallo yabita dashi yace dear why?"   tsaki taja tatashi tayi hanyar waje, runtse idanuwa yayi."  kafin lokacin harta fita palour, dasaurii yatashi yabita, har yak'araso wajan ta, fincikota yayi yana cewa ina zaki je?"
D'agowa tayi ta sharara masa marii sannan tace gidan ubanka zanje, dasaurii tak'ara cewa nace gidan ubanka zanje, ta fad'a tana juyawa zata k'ara tafiya, mutuwar tsaye marshall yayi a'iiya saninsa *hanna*  bazata iya aikata hakanba."  afili ya furta something strange is happening."  k'arasowa yayi kusada ita yajawaota yariqeta gamm, ihuu tafara tana kwararo masa ashar tana dukansa harda cizo, ganin abunna ta yawuce tunaninsa yasashi kalleta tabaya, yanufii shashin ummii hankali tashe." 


   Kilishii zaune ad'aki sai zurga-zurga takeyi, ganin bazata iyayin hak'uri bane yasata d'aukan wayarta takira ta, tana d'auka ko gaisuwa babu tace nifa najii shiru."  haryanzu bbu wani labarii wannan matsiyaciyar bata haukace ba."    daga cikin wayar najii ance, kekuwa mai kikecii nabaka yana zuba?."  ya tabbatarmun zata haukace amma gaskiya bazatayi hauka tu6urum ba, dan suna yawan yin addu'a, eh kmadai menene tayi, inyaso saimu 6atarda ita." 
Ahaka takatse wayar."

  Yana shiga baisamu ummii apalour ba ad'aki yasameta da gudu yak'araso kusada ita cikin tashin hankali yafara cewa ummii *hanna*  ummii *hanna*  batada lpy, dasaurii ummii tamiqe ganin halinda d'annata yake ciki, dukda bbu hawaye afuskarsa, amma kuma cikin kwayar idanuwansa ta fahimci irin tashin hankalin yake ciki."
Itama da saurin ta surii himarinta ta bishi abaya, danshi yarigada ya futa."
Tsakanin shashin ummii danasu *hanna* danisa amma few minute ne suka kaisu."
Bud'e k'ofan yayi suna shiga, aikuwa sukayi turuss ganin yanda jinii yake zuba jikin *hanna* ga baki d'aya tayi caka-caka da falon."
  Duk ta yayyanka jikinta da gilasai, jin bud'e k'ofa yasata juyawa, aikuwa tana ganin su, ta jefo glass na humra dake hannunta, tarewa marshall yayi da hannunsa, nan da nan, hannun yatsage jinii yafara zuba, dagashi har ummiin kanta sukayi yana zuwa kuwa yariqeta kamar wanda take jira ariqeta, tayii luuu tafad'ii hannunsa, sumammiya."  kuka ummii tafashe sosai tanayi tana magana."  futada ita mota mukaita asibitii."  cikin tsawa tace nace maka mufice asibitii."
Waje yayi da ita ummii nabinshi abaya tsabar tashin hankali tunkafin yazo har an bud'e masa mota tsabar irin kirin da yakeyiwa sajen."
Ganin marar lafiya yasa sajen yanufii asibitii direct."
Suna isa aka karbeta ciwukan jikinta akafara, mata dressing, sannan aka ce tana buk'atan jini dan yazuba ajikinta sosai."
Ajikin marshall aka eba aka fara k'ara mata."
Dakyar yayarda shima aka masa dressing ciwonsa, dan yafii jin zafin ciwon jikin *hanna*, ummii Dakyar tasashi yakoma gida yaje yagayawa mai martaba, dan ita bazata iya tafiyaba, alokacinma jimawa kad'an tashare hawaye jimawa kad'an tashare hawaye." Doctor yasanarwa da momy cewa *hanna* tana d'aukeda juna biyu na wata d'aya kacal, kuma sunyiii iya bincikensu basu samiii wata matsala akwakwalwarta ba."
Kuka ummii tarushe dashi na tausayin *hanna* da kuma abunda yake cikinta."
 Roqon Doctor tayi da karya fad'awa marshall, dan batasan irin tashin hankainda zai shiga cikinba."
Kwanan *hanna* biyu a asibitii amma abuu gaba yake dad'awa, ganin haka yasa ummii tayanke shawarar sanarda umma, aikuwa ranar sunshiga tashin hankali barinma hameeda da yaya jalal."  umma ne tahana fad'awa mama dan tana gudu mata tashin hankali."  lokacii d'aya ummii da marshall suka zabge dan kowannensu cikin damuwa yake."
Idan kagansu zaka d'auka sune majin yatan."
Ganin ciwon yak'ii warkewa yasa mai martaba yacewa affan yaje yad'auko modibbo, sukuma likitoci sun bada shawarar fita da ita wajan likitan kwakwalwa."
Dasaurii affan yafito daga shashinsa, wuce kilishii yayi afalo tana zaune, kwala masa kira tayi,  kai inazakaje?"  umma wallhy abbane, yace ind'auko modibbo inkaishi asibitii, koda abunda zaiyii akan ciwon, matar yaya yareema,"
Gaban ummane yafad'ii, had'erai tayi tace maza jeka kad'aukomin intisar tana gidan hajiya salamatu, waro ido yayi yace umma, abban,,,, tsawa tadaka masa, kai da'allah rufamin baki, kaje kad'aukota tunda bawai guduwa modibbo d'in zaiyii ba."
  Fita yayi ransa yana suya, yana fita takira wayan kawarta, tace ke abu ynason kwabewa, yanzu kiyi saurii kafin yaronnan yaje yadawo, a6atarda ita kawai tabar k'asar ga baki d'aya sannan, sannan arufe bakinta kada hankalinta yadawo bazata iya bud'an baki tafad'ii daga ina takeba."
  Daga cikin wayan aka ce mata kinsan shifa baya aikii saida sharad'ii, kilishii tace koma menene nad'auka, yanzu fa ko 30 minute kada ak'ara takashe wayan."

To be continued

Ur's
     Z33iiyyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

Writing by
     *©zaynab bawa*
*(Z33iiyyb3rw3r)*

_Like my page on Facebook=zaynab  BAWA novels_

 _Join my group on Facebook= ZAYNAB BAWA NOVEL'S_

*Manzon Allah sallalahu alaihii wasallam yace, ku karanta suratul kahfii ranar juma'a, Allah zaicika maka haskenta har wata juma'ar, zaka kasance cikin haske da farinciki."*

================

*Godiya masu kirana danjin mai jiki, Alhmdllhy jiki dasauki, siyama na amsa gaisuwarku tana godiya, nagode sosai queen najii dad'in, kulawarki sosai, Nagode all, Allah yabar k'auna."*

.

================

Page 85

*
  Umma ce zaune itada ummii cikin aminity, suna hutawa, sunfita sunbar *hanna* ita kad'ai hameeda kuwa tatafii yin abinci, ko *hanna* zataci dan idan akayi sa'a, dan wani lokaci akanyi sa'a ta d'ancii abincin ko kad'an ne."
 *Hanna* na hango tafito daga cikin d'akin da take, doguwar riga ajikinta, kanta ko d'an kwali bbu."  hankalin su ummii kwata-kwata bayi wajan, kamar wanda wani abun yad'auke musu hankali."
Har *hanna* tafice acikin wajan bbu wanda yajuyo, haka harta fice daga harabar asibitin bbu wanda yatsayarda ita, dukda alamomii dayawa ajikinta yanuna ba cikkken hankali atattare da ita."
  Tana fita ta tsaya atiti kamar mai jiran abun hawa, wata taxi ne tatsaya da wani mutum aciki mai wata irin halitta,  wanda kollonsa kad'ai zai saka cikin shakku, kayi tunani koba mutum bane."
Nikaina zuciyata tafii kar kata, dacewar aljanine, magana yayi cikin wata irin murya, mai rikitarwa yacewa *hanna* shigo muje, bbu musu hanna tabud'e motar tashiga gidan baya, nan kamar wata walqiya yaja motar yayi gaba."
Kusan awah biyu suka shud'e."
Can nahango *hanna*  tana tafiya duk k'afofinta sun fashe alamun tayi tafiya sosai."
Tana tafiya har tahau kan titi, unexpected wata mota k'irar jeep tazo wucewa ganin mutum akan hanya yasa tayi gefe da niyyar kaucewa, amma inaaa, sai dayazo dabb kamar wanda aka tunzurata, saijin kawai sukayi sun bigeta, salati mutanen cikin motar sukasa, nan suka samii waje suka tsaya, matan dake baya cikin motanne sukayi saurin fitowa sukayi kanta."  ganin jinii yanabin kanta yasasu, kwalawa wanda yake driving d'in kira, dasaurii yafito, wani saurayine kyakkyawan gaske, duk wani alamu najikinsa yanuna, cewa shi cikkken bafulatani ne, dan da fullan cinma suke yin magana, amma saidai yanda najii suna fillancin gabaki d'aya ya banbamta, dana k'asar nigeria, kinkimanta yayi yasata acikin motar dake seat ukune da ita, asibiti suka nufa lokacii guda, dake manyan mutanene ba'atsaya bincikeba aka k'ar6eta aka shige ciki da ita."
Basu dad'eba aka futo aka shaida musu cewa, jikin alhmdllhy bataji, wani ciwo sosai ba."
Sannan d'an dake cikintama lapynsa klau."
D'aya matarne tadubi, D'ayan wanda da'aalamu tagirmi D'ayan, tace, diddii naga kamar k'qramar yarinyace kuma budurwa."
Allah dai yasa bawasu mugayen bane suka mata fyade suka yasarda itaba."   nisawa wanda aka kira da diddii tayi tace,"
Allah shi yabarwa kansa sanii hussentu,  abunda yakamata yanzu ina shii sadiq yashiga?" nisawa hussentu tayi Sannan tace,"  ya tafii k'ar6o maganinne, to Allah yadawo dashi lpy."
Bayan yadawo da 1hour *hanna* tafarka, duk iya tambayar duniyarnan anyi mata amma takasa bud'e baki tafad'i ko kalma d'aya,"  da suka isheta da zantuka kawai saita sheqe musu da dariya, harda kyakyatawa, ganin haka yasa suka nemi likita."  yana zuwa yafara dube dube, nan aka shiga da ita d'akin na'urorii, iya bincikensu baigwada musu akwai wata matsala, akwakwalwarta ba."
Hakan yafito yashaida musu sunyii matuk'ar mamaki, tunda duk wani alamu yanuna ta6in hankali attatere da ita." 2days aka sallamesu gidansu suka nufa."
Nan diddii tabuk'acii sadiq daya d'auki pics d'inta yazagaya ya aika gidan redio, television, dasauransu, ko za'a dace, Hakan kuwa akayii, and'aukii 5days sadiq yana sanarwa, amma bbu ko batan hanya da wani yazo dan nemanta."
Agajiye liqis sadiq yadawo yazauna, wata mata wanda daga ganii y'ar aikice takawo masa ruwa, bai iya shan ruwanba, yadubii diddii yace,"  diddii duk iya cikiya nayishi, aksarnan bbu yanda bankai cikiyaba amma bbu."
Nifa atunanina yarinyarnan ba y'ar k'asar camroon bane, camroon na maimaita cikin raina😳🙆,
Allah kawai yakamata mu miqawa komai mucigaba da mataa addu'a, kuma muna nema mata maganii."
Diddii bata iya cewa komai ba sai Allah yabata lpy."

   Basu ankara da cewa *hanna* batanan ba saida hameeda takawo abincin tazo da samesu, aresting room d'inda suke zaune tace,"  Umma nakawo abincin, dasaurii ummii tamiqe tace barina je toh ko zata cii na rarrasheta, d'akin tanufa tana shiga taga wayam, koda mamaki ne yacikata dasaurii tayi toilet nan ma bbu kowa, fitowa tayi nufii gun Umma tana cewa kinga yanda *hanna* tayine? Dasaurii Umma tamiqe tace banganeba? Aimuna zaune dake anan, *hanna* bata d'akinne? Ummii bata tsaya bata amsaba, tawuce tafara dube dube a cikin asibitin, Umma ma tabii bayanta jikinsu duk rawa yakeyi." duk girman asibitin acikin few minute suka zagayeshi, bbu ita bbu dalilinta, bakin gate suka yi suna tambayar masu gate ko sunga fitarta,"
Aikuwa sukace basu ganiba, dan kamar wanda aka rufe musu ido."
Waje sukayi suna tambaya nanma bbu wanda yace yaganta, sunshiga tashin hankali kam sosai, kowacce kuka takeyi bbu mai lallashin wani."
Wani d'an tsoho dazaikai 80yrs, wanda tun fitowar *hanna* shi kad'aine yalurada ita kasancewar, yanada d'an bud'edd'en ido, yamatso kusada su yace,"  bayin Allah wa kuke nema haka?." dasaurii Umma tace y'armuce tafice daga asibitin kuma kowa yace baiganta ba." shiru yayi nawasu lokaci kafin yace," kafin yace naganta da doguwar riga ajikinta, dasaurii ummii tatashi tace itace wallhy itace."
A'ina take?" girgiza kai yayi yace kucii gaba da addu'a, Allah zai bayyanata, Su kansu wanda suka d'auketa basufii k'arfin Allah ba."  zaro ido sukayi mekake nufii kenan da Hakan?"  wata y'ar dariya yayi yace, ai addu'a da kuke yi, da wanda mijinta keyi, da wanda ita kanta keyi yasa basu cutarda itaba, yanzu haka tana hannun mutanen arziki, idannace ku kwantarda hankalinku nikaina banmuku adalci ba." kawai kuyita mata addu'a, bbu abunda yafii k'arfinta, atake ummii tazube awajan sumammiyya, dasaurii sukayi kanta, dai-dai tsayuwar motan abban wanda yad'auko middibbo,"
Dasaurii yak'arso baitsaya tambaya ba, ya kinkimi ummii yayi cikin asibitin da ita, Umma kuwa alokacin suka nemi mutuminnan samada k'asa suka rasa, dasaurii sukayi ciki, duk iya tambayar affan bbu wanda ya iya bashi amsa,"  ganin Hakan yasa yak'ira marshall ya shaida masa yazo hospital."

  _Kuyi hak'uri kuyimun uzuri, bayadda na'iya, amma in sha Allah cikin month d'innan zangama_

To be continued

Ur's
   z33iiyybawa

*BIBIYATA AKEYI*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

Writing by
     *©zaynab bawa*
*(Z33iiyyb3rw3r)*

_Like my page on Facebook=zaynab  BAWA novels_

 _Join my group on Facebook= ZAYNAB BAWA NOVEL'S_

  ```Dan Allah kada mu gaza wajan taimakawa y'an uwanmu akan buk'atunsu, dan Allah damuwar wasu ta Zama tamu damuwar, koda bazaka iya taimakawa, ta wani hanyarba, yanada kyau, ka taimakeshi tahanyar addu'a, dan kaima watarana, zaka buk'acii ataimaka maka koda tahanyar addu'a ne danshine babban tainakon da mutum zaimaka aduniya."  nidai zaynab bawa ina buk'atar addu'oiinku daga bakunan ku masu albarka."
Balaifii bane kuma ba gazawa bane ko kankastar dakai neman taimako na addu'a ba, tabbas bakasan bakin wani ba, danna roqii alfarmar addu'a awajenku nasan zakuyimunne, nagode."```

================

  ```This page is dedicated To you, FATIMA IBRAHIM(MUNEERAT)
and SAWWAMA QAWWAMA (doughter) Allah yabarni tare daku har abadan."```

.

================

Page 86

*
  Jin kiran gaggawa daga asibiti yasa hankalin marshall masifar tashi, tun d'azu kawai yana meeting ne amma kuma hankalinsa na hospital, yarasa dalilin dayasa tunda yatashi gabansa ke fad'uwa hakanne yasa dakyar sanda ummii tasaka baki kafin ya halarcii meeting d'in."
  Ana cikin yii ko excuse bai d'aukaba ya fice, soldier's suna kallonsa sukayi saurin bud'e masa k'ofa, dasaurinsa yashige, drivern yafara driving har suka iso hospital d'in, dasaurii ya fito ya nufii ciki suma suka mara masa baya, sanda yazo bakin k' kofar shiga d'akinda aka kwantarda *hanna* ne sukaja suka tsaya, shi kuma yak'arasa, ganin ummii akan gadon marassa lpy dasaurii yak'arsa yana tambayarta mai yafaru?"
Ummii wani abune yasameki?"  maimakon naga *hanna* naganki kota samu lpy ne?"
Muryan affan ne dake bayansa yakatseshi, yace yaya wallhy tund'azu nafad'a musu su sanarda ni abunda yake faruwa amma kuka kawai sukeyi bbu wanda yakulani."
 Dasaurii yakuya wajan Umma yana cewa Umma wani abunne yasamu *hanna* Umma dan Allah kifad'amun, jijinsa rawa kawai yakeyi."
 Kawarda kai gefe Umma tayi bata iya bashi amsa ba, gabaki d'aya tausayinsa ne yayi mugun kamata, kuka kawai takeyi, yajuya zuwaga hameeda dake k'asa numfashinta yana kok'arin d'aukewa, ai kafin yak'arso yasamu damar tambayar ta numfashinta yad'auke cakk, nan ta sulale k'asa sumammiyya."
Muryar ummii ne ta daki dodon kunnuwansa,
Tana cewa Abdallah *hanna* ta6ata wallhy bamusan yanda takeba."
Zuciyarsa ne tayi wani irin bugawa take wani abuu ya tunkaroshi da k'arfii ak'ok'on Zuciyarsa, abun tasowa yakeyi har wuyansa, tashi d'aya yayi wani tarii gudan jini ne yafad'o wanda duka d'akin sanda ya suka jijjiga, dasaurii affan yayi kansa yana kiran sunansa amma, d'aga masa hannu kawai yayi yatsaya cakk, yayinda shi kuma yaja da baya, yajingunu da bango, yazauna ya sunkuyarda kansa, d'akin yad'auki 10 minute ahaka bbu wanda ya'iiya magana, ga hameeda asume marshall kuwa ban isa ince yana sume ko yanada rai kokuma baudashi ba."   ga ummii itama hankalinta yayi masifar tashi naganin aman da marshall yayi."
Umma kuwa tadawo mutum mutumii."
Haka ummii tasauko tanufii marshall Tana kuka tana masa magana amma ko kiftawa idanuwansa bayayi, haka tayita jijjigashi ko motsi bai yiba."
Zama tayi kawai agabansa, tana kuka, ganin abunda ke faruwa, yasa affan ficewa yasanarda mai martaba, ba'ad'auki lokaci ba ya'iso, hospital d'in,

Yana zuwa ganin abunda ke faruwa, yasa hankalinsa mugun tashi, nan aka kira doctor's aka tafida hameeda, yayinda shikuma marshall mahaifinsa yayi kansa yana masa magana, amma ko motsi baiba."
  Ganin haka yasa mai martaba dakyar ya lallashi ummii aka tafii da ita gida, Umma kuma tana wajan hameeda."
Awah ukuu curr marshall yad'auka awannan hali."
Wata ajiyar zuciya mai k'aran gaske ya sauke, itane tajawo hankalin mahaifinsa, k'arasowa kusada shi yayi yana kiran sunansa, d'agowa marshall yayi da jajjayen idanuwanshi, yatsare mahaifin nasa da kallo kamar wanda yau yata6a kallonsa."
 Nisawa mai martaba yayi yace, yareema tashi mutafii gida, girgiza kai yayi yace A'a abba bazan tafii ba, zata dawo, zan jirata."  girgiza masa kai mai martaba yayi yace Zamu nemota kataso mutumii, zaiyi magana mai martaba yayi saurin katseshi yace, kada muyi haka dakai, yareeema ka tashi mutafii, har indai nine nahaifeka kabii umarnina, miqewa yayi yana Shirin fad'uwa mahaifinsa yayi saurin riqoshi, haka yafita dashi daga cikin asibitin yariqe hannunsa kamar k'aramun yaro, shikuma yana ta kalle kalle, haka mai martaba ya sashi amota suka nufii,  gida."

   *PLZ KUTAYANII DA ADDU'A WALLHY INACIKIN DAMUWA SOSAI ,😭😭😭😭😭 INA CIKIN MATUK'AR DAMUWA , DOLE INA BUK'ATAR ADDU'A DINKU , KUYIWA GIRMAN ALLAH KUJII TAUSAYINA KUMIN ADDU'A ."  KARKU GA TYPING YAYI KAD'AN AYANAYIN DA NAKE CIKIMA DA BAZAN IYABA, BUK'ATAR ADDU'A DIN KU DA NAKEYI NE YASA , NAYI , DAN AllahT KADA KU MANTA DANI ."*
*KU D'AGA HANNU KU ROQAMIN ALLAH YABIYAMUN BUKATUNA.*

  *Kuyi hak'uri ko zakuga mistake, wallhy dada rana nayi typing da yayi yawa amma yanzukan sai neman gyaran ubangiji."*

To be continued

Ur's

     Z33iiyyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

Writing by
     *©zaynab bawa*
*(Z33iiyyb3rw3r)*

_Like my page on Facebook=zaynab  BAWA novels_

 _Join my group on Facebook= ZAYNAB BAWA NOVEL'S_


```Manzon tsirada amincin Allah su tabbata agareshi Yana cewa Allah ya jikan wanda ya yi sallar nafila raka'a hudu kamin la'asar.```

```Manzon Allah tsirada amincin Allah su tabbata agareshi yace, Wanda da yi Sallar nafila a cikin duhu inda bawanda zai ganshi to Allah zai' linka masa sau ashirin da biyar na sallar da zai yi wani ya ganshi.```


```Manzon Allah tsirada amincin Allah su tabbata agareshi ya ce, Wanda yayi sallar walha (Sallar hantsi/Luha) rakaa hudu kuma yayi rakaa hudu kamin sallar laasar, Allah zai gina masa gida a cikin aljanna.```

.
================

Page 87

 *
   Fad'in irin tashin hankalin da marshall yashiga wannan ma tsayawa, bata lokaci ne, gabaki d'aya yazama wani iri,  bud'e idanuwansa ma wahala suke bashi, balle aje ga cin abincii ko wani abun."  nauyii idanuwansa ke masa, alokacinne yak'ulla mugun alaqa da ciwon kai, wanda akullum kansa ke barazanar tsagewa gida biyu,
Baida sukunii, baida wani sauran kwanciyar hankali, kullum cikin zullumi da tunanin yanda *hanna*  tashiga yake, tunaninsa ko awana irin hali take, baisani ba." a kullum har wani hucii ne mai d'umi yake fita daga jikinsa, idanuwansa kuwa idanya bud'e yanda kasan garwashi, har shakkarr bud'esu yakanyi, dan har indai mutum yana kusadashi sayyya razana,  sa'ii-sa'ii yakanyi aman jini, amma bai bari kowa ya lura ba, koda sallah ma ad'aki yakeyi, ummiii tayi kukan harta gajii,

   Ganin bbu Wata mafita yasa umma takira mama akan tanason ganinta idan zata samu dama suzo suda baba, dafarko mama tayi tunanin su hassana da hussaina,
 Hakan tafad'awa umman, amma umma tace mata tabarsu ma ammah tazo, ganin zancen mai k'arfii ne yasa tasanarda baba, kiran k'aninsa yayi awaya, abba yacewa baba gaskiya yanadakyau zuwannasu, haka suka shirya washe garii suka d'auki hanyar kano, sha d'aya tamusu acikin garin kano, gidan Abba suka wuce kai tsaye, ganin Wata irin ramar da umma tayi mama ta matuk'ar tsorata, dasaurii tak'arasa kusada ita, riqo hannunta mama tayi cikin kid'ima tafara magana, yaya menene yasameki haka?"  yaya dama bakida lpy ne baki fad'amunba?, girgiza mata kai umma tayi kawai hawaye nabin fuskarta, da sallama abba yashigo falon, ganin umma na hawaye yasa yace ashsha assha, yanzu daga zuwansu kintaryesu da kuka, hava da Allah wai kekam bakyada hakurii ne, kuma bakida juriya, hava, idon mama har yacika da hawaye tashi d'aya yafara zubo mata takalli abba tace dan Allah kafad'amun ko wani abun ne ke damunta, rintsawa abba yayi kafin yace, kuzauna ku huta kafin namuku bayani, girgiza kai mama tayi tace, nidai bazan iya wani hutawa ba, bayan Ina kallon y'ar uwata cikin wani hali, juyawa abba yayi batareda yak'ara cewa komai ba, yanufii babban palour wajan baba."
  Duk yanda mama taso tambayar umma abunda ke faruwa takasa sanarda ita, abba baifii 10minute da tafiya ba ya leqo yace, sutaso su tafii, tunda suka d'auki hanya bbu wanda ya iya magana, ganin sun nufi fadah yasa gaban mama da baba yayi mugun fad'uwa tunainsu d'aya badai wani abun bane yasamu *hanna* sunfii ma karkata da ko batada lpy ne, har suka isa fada, bbu wanda yatofa ko da kalma d'ayane, dama ansan da zuwansu, dan haka falon mai martaba, aka sauk'esu marshall na kwance tun shigarsu afalo, amma bai iya d'aga kansa ya kallesu ba balle susaran zai gaidasu abun bak'aramun mamaki yabawa baba da mama ba, banda umma da abba dan dama sunsan irin halinda yake ciki, tunda *hanna*  ta6ata bai k'ara furta ko kalma d'aya ba, ummii da mai martaba ne sukayi sallama suka shigo falon daga d'akinsa, waje mai martaba yasamu yazauna, sannan yabawa su abba hannu suka gogaisa da addu'a yabud'e taron sannan yafara magana."
  Kusani cewa Duk wani abunda yafaru muqadda rine daga Allah, kuma Allah subhanahu Wata ala yace, la yukalliful lahuu nafsan illa wus'aha, yace Allah baid'aura rai abunda bazata iya ba."  sannan Kusani kowani d'an adam da irin hanyardaa Allah ke jarabtarsa, sai dai muyi addu'a Allah yabamu damar cinye tamu jarabawar data fad'o mana, sannan d'aukan qaddara yana d'aya daga cikin cikon imani, musani Allah baid'aura mana abuu har sai dan yagwada imaninmu
 Yaga yaya jamuyi dan yajarabcemu, tundaga wannan lokacii ummii tafara hawaye tana goge hawayen idanuwanta, nan mama tak'ara karyewa sosai tace," ku gayamun maiya samu *hanna*  mu musulmaine tabbas zamu kar6i kaddar mu hannu bibbbiyu, zamu riqe wannan jarabawa,  dakyau mumata kyakyawan duba yanda idan skamakon mu yatashi futowa zamu samu sakamako mai kyau."  ita kanta duniyar nawa take?"  kan ummii nak'asa takasa d'agowa takallesu tace *hanna*  ta 6ata wallhy *hanna*  ta6ata, gaban mama ne yafad'i rass, wani irin jirii ne yafara ebanta, amma kuma duk dauriyarta ta tattaro, da mamakin mutanen wajan gabaki d'aya, murunushine kwance afuskarta, sannan cikin dakiya tace, kada ku damu da sanin Allah in sha Allah zai bayyanata, addu'arda zamu mata Allah yasa tana wajan kyakyawan hannu."
Shima baban dukda cewa abun yadakeshi addu'ar kawai yayi, share hawayen idonta umma tayi sannan tace, Aisha abun damuwar d'aya shine *hanna*  bata cikin hankakinta lokacin da ta 6ata, *hanna* tahad'u da ta6ewar hankali, abunda yasa bangaya miki ba, bawanda yad'auka, zata dad'e cikin wannan jinyar, dan Allah kiyi hakuri, girgiza kai mama tayi tace hava yaya wani irin hak'urii kike bani?"  bayan kuma mahaifanta ne, nasan kulawarda zaku bata, ko da inanan bazan bata hakanba."

   Inada yak'inin kunfinii jin zafin 6atan nata, dan Allah kudena fad'in haka, kum,,,  tarinda marshall yad'aukane  yasa tayi saurin yin shiru, bai dad'e yana tarinba yalafa, mama ta kulada yadda wani abun da yafito abakinsa, amma yasa hannu yarufe, duk wannan abunda yakeyi, tashi mama tashi tak'arsa gabansa, batayi magana ba, kawai tasa hannunta tad'ago nasa hannun razana tayi ganin wani irin bak'ik'irin d'in jini, ga lebb'an bakinsa ma duk yaa6ci da jinin, dasaurii tajuyo tallaeshi tace abdallah tashi mutafii asibiti bakada lpy fa, shiru yake kamar yanda yasaba idan anmasa magana, ummii ne tace, kirabu dashi kawai ko zaki kwana kina masa magana ba kulaki zaiyii ba."
Koda bazai kulaba yakamata akira doctor yadubashi, umma tace, mamane ta amshe da cewa aman jinifa yakeyi, sai alokacin kuma duka hankalinsu yatashi, dan duk cikinsu bbu wanda yasan yana wannan aman."
Dasaurii mai martaba yad'aga waya aka kira likita, ba'a dad'e ba ya iso, dube-dube yafarayi, nan yajuya yakellesu yace, idanda hali asibiti yakamata mutafii, dan likitoci da damane yakamata su kasance akansa ayanzu haka, babane yace, doctor bafa zaije ba, ka kira likitocin nan suzosu, hakan kuwa akayi, nan yakira doctor's dakuma nurses, sukazo da motan hospital, hadda gado, buk'ata sukayi akan afita abarsu ad'akin, hakan kuwa akayi, sun d'auko awowi masu yawan gaske, kafin su fito, ababban falon mai martaba suk zaune, dukansu, anan likitocin suka semesu, bayanii likitocin sukayi sosai yanda hankalin mutanen falon gabaki d'aya ya tashi,   d'ayan likitanne yace, gabaki d'aya zuciyarsa ta buga, kuma alamu yagwada ta dad'e cikin wannan halin, dan yanda muka duba tqkai kaman 2weeks, gaskiya abun yabamu matuk'ar mamaki, bamu ta6a kallo, kuma ko alabarii bamu ta6ajin wanda zuciyarsa takai wannan stage kuma yarayu ba."
Amma sai daiamakinmu ragaggene, idan mukayi la'akari da wanene shi, ayanzu haka dole yana buk'atar taimakon gaggawa daga nan, kafin ad'aukeshi, zuwa k'asar waje, abba ne yace yanzun abunda za'ayi kakira ambulance daga asibitin ku, akaishi can, sai ayi masa alluran bacci, dan jinya anan bazaiyiwu ba, nisawa d'aya litikan yayi yace, alokacin da zamu fara dubashi bbu irin alluranda bamuyi masaba, amma bawai yayi bacci bane kokuma hankalinsa yagushe ko d'aya, ahakan mukayi aikin, yanzu haka idonsa biyu sai dai kawai ba'a bud'e suke ba, sannan duk abubuwanda akeyi yanajii."
Ummii kam takasa magana, sai mamane tayi k'arfin halin cewa, kud'aukeshi ahaka, mutafii tare tafad'a had'eda miqewa, nurses ne suka tura gadon har zuwa gaban ambulance, tareda mama suka shiga, aminu kano suka nufa, nan aka kaishi aminty,"
Adakinda aka kwantardashi, mamane zaune itada umma da ummii,"
Satin marshall d'aya yad'an fara samun lpy, lokacin yakama 3weeks kenan da 6atan *hanna* mamane ke jinyarsa asibitin, tana nuna kamar bata damu bane amma zuciyata nacike da kewa da kuma zulumin hainda y'artata take ciki, baba kuma yakoma, gabaki d'aya hospital d'in sanda aka zagayeshi da soldier, balle d'akinda yake kwance, doctor's ne suka samii mai martaba, akan ad'aukeshi daga wannan hospital d'in zuwa k'asar waje, dan sai sunyi kamar zasu shawo kan matsalar sai abun ya faskara, shawararda mai martaba yayanke kenan, shiga d'akinda aka kwantardashi yayi, yana kwance kamar kullum ba umm ba um umm, mai martaba yakalleshi sosai sannan yadubii mama da ummii yace, yaronnan kawai xan fiddashi ne hankalina yakasa kwanciya, haryanzu bbu wani takakkammen halinda yake ciki, yadubii mama sannan yace zankira Alh muhammad na fad'a masa zuwa jibi zaku wuce."
  Muryarda yau watansu guda kenan, wanda suka dad'e basu jitaba, ne yakatsesu da cewa, ni bayanda zanje, ku barni anan, haryanzu ban fiddaran dawowar *hanna* kwana kusa ba."
Zaro idanuwa sukayi suna kallon ikon Allah."

To be continued

Ur's

        Z33iiyyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

Writing by
     *©zaynab bawa*
*(Z33iiyyb3rw3r)*

_Like my page on Facebook=zaynab  BAWA novels_

 _Join my group on Facebook= ZAYNAB BAWA NOVEL'S_

.


```Manzon Allah tsirada amincin Allah su tabbata agareshi  ya ce Wanda ya yi sallar nafila rakaa goma sha! biyu tsakanin dare da rana Allah zai gina masa gida a cikin gidan Aljanna.```


```Manzon Allah tsirada amincin Allah su tabbata agareshi yace, Wanda ya kiyaye yana yin nafila raka'a hudu kamin sallar azahar da kuma raka'a hudu kamin sallar la'asar to Allah zai haramta masa shiga wuta.```
.

     ```Manzon Allah tsirada amincin Allah su tabbata agareshi yace, Wanda yake karanta ayoyi goma da daddare to baza'a rubuta shi cikin gafalallu ba, wanda ya ke karanta ayoyi dari to za'a rubuta shi cikin masu bauta ga Allah, wanda kuma ke karanta ayoyi dubu a cikin dare kullum to za'a rubuta shi daga cikin masu arzikin lahira.```
.

   ===============

Page 88

*
   *Hanna* harta fara sabawa da mutanen gidan dan da farko ko abincii suka bata, baxata ciba, yanzu hartakan zauna idan sunyii abun dariya tayi tayi nawuce hankali,"

  Hussentu ne tadubi diddi tace, diddi wallhy kullum idan naga yarinyarnan tausayi take bani, bansan su inne da yasa ishaq idan kusa dawo wani irin kallo zasu mata ba, bansan da Wata manufa zasu d'auketa ba, su halinsu yafice daban, wallhy diddi kaman bakene kika haifii yaya ishaq ba, kamar innece ta haifeshi, diddi batace komai ba, tacigaba da cewa,  wallhy inason yarinyarnan har cikin raina, jinakeyi kamar y'ar uwata, Allah idan sukace tabar gidan saidai inbita mutafii tare, diddi dai shiru tayi saican tace wallhy nima inason yarinyarnan, sosai, banjin zanrabu da ita idan bawai tadawo hankalinta bane tanemi komawa gun danginta ba, yanzu tashi kije kidubamin metakeyi, kotacii abincin, tashi tayi tace to, azaune tasamu *hanna* tace, kincii abincin?"
Juyowa *hanna* tayi amma batace komai ba,"  ganin abincin tayi agabanta furr tak'ii cii, riqo hannunta tayi tace taho muje, tashi tayi tabita, dan yanzu komai nata da sauk'ii bandadai tayita dariya ba, bazaka ta6a ganewa da hauka ajikinta ba."
Tana zuwa tace diddi kinga tak'icii furr, dubanta diddi tayi da kalar tausayii tace, kinsan tanada juna biyu bakowani irin abincin suke so ba, riqe hannunta taje store da frigde kinuna mata koda abunda zataso, idan tagani zata nuna, jan hannun nata tayi zuwa frigde."

================

 Da mamaki suka tsaya suna kallon sa, idanuwansa sunanan arufe kamar kullum, maganar ma bazakayi zaton daga bakinsa tafito ba,
Dama asali miskilancin sane yatashi, shiyasa yak'ii magana bawai dan bazai iyaba, bakuma dan maganar ta gagareshi ba."

  Mama ta amshi maganar bakaso akaika to wani dalili zaisa bazaka cire damuwa aranka ba kasamu lpy, abdallah kayi tawakalli ga ubangijinka, kasan cewa jarabawace yad'aura maka, nan tayita masa nasiha, mai martaba ne yace ka shirya gobe da tafiyar dan nan d'innan bawai naga wani cigaba bane,  idanuwansa arufe yak'ara cewa, har indai sai nafita kafin nawarke tom bazan ta6a warkewa ba."
Ummii ne takalli mai martaba tace dan Allah kabarshi anan d'in, tunda yayrada zaicire damuwa aransa."
Mai martaba bai ce komai ba yafuce, office d'in likita yanufa, yana shiga litikan yatashi yana gaidashi, yana cewa ranka shi dad'e da kanka? Aida ka aika nazo, mai martaba bai kulashi ba yasamu waje yazauna sannan yadubeshi yace, nafasa fita dashi, Ina anan zaisamu kulawa sosai?'
Nisawa likita yayi yace zai samu amma saida taimaknku, dan mukad'ai abun yagagaremu, bazamu iya mukad'ai ba, dole aringa d'auke masa damuwa, sannan idan anan ne jinyan 2month zaidaukemu idan ak'asar wajan ne baifii 3weeks ba,
Mai martaba yace bbu komai, hakan kuwa akayi, anan aka fara jinyarsa, mama takanje bauchi tadawo,
Kuma kullum takansashi agaba da nasiha, harya fara cire damuwar,
Saidai abunda ba'a rasawa yanzu rashin magana harta nunka nada, dan saikayi sau 5baikulaba, watanshi 1yasamu lpy, amma sanda jinyarda suka yanke mata 2month dan yanda suka kalli yanayinsa mai karfin zuciyata, amma mafii akasarii akanyii 3-4month ana jinya, mai martaba ne yahana asallamesu har sanda yacika 3month cifff a hospital."

===============

  Cikin *hanna* yad'an tasa kad'an, amma kana ganinta zakaga alamun tanada ciki, gawani kyau da takara, abun mamaki harda k'iba, dan yanda take samun kula,

Yaune takasance ranarda su ishaq ta inne zasu dawo, maimakon murna sai suka shiga fargaba da zullumii,"
Wasu rantsattsun motocine suka fara shigowa gate d'in, diddi ta kalli Hussentu wanda lokacii d'aya duka gabansu yafad'i tace, yi maza kisakata ad'akinki ki kulle dasaurii tajata suka shiga d'akin."

To be continued

Ur's
    Z33iiyyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

Writing by
     *©zaynab bawa*
*(Z33iiyyb3rw3r)*

_Like my page on Facebook=zaynab  BAWA novels_

 _Join my group on Facebook= ZAYNAB BAWA NOVEL'_

.

================

  Page 89

*
   D'aki takaita, sannan ta kwantarda ita, tace bodd'i zauna anan, kijirani karki fito kinji, kamar wata mai cikakken hankali tad'aga mata kai."
  Yawwa bodd'i na kinada jin magana tashafo fuskarta sannan tafice."
  Wani kyakkyawan saurayi ne yafito daga motar, wqnda duk kyawunsu hussentu danake gani sainaga har sadik yafii kyau, hannunsa d'aukeda wata y'ar k'aramar yarinya wacce bazatafii 4yrs ba, gabaki d'aya saurayin bazai wuce sa'ar marshall ba."
  Ko kad'an fuskarsa bbu annurii dan baiyi kama da masu dariya bama, dasaurii diddi tak'arasa ta d'ayan kofan, ta sa hannu ta bud'e, wata y'ar dattijuwa, nagano, kamar su d'aya sakk, da d'an saurayin daya fito daga motar, wasshe baki diddi tayi tana cewa, usse inne, wanda aka kirada, inne ta d'aga kai tayi kawai alamun ta amsa, daga yanayin matar yanuna tanada jin kaii sosai, tafiya tafarayii, diddi nabinta abaya, dasaurii hussentu tafito ta nufii yayanta, yarinyar datake hannunsa tamiqawa hannu amma yarinyar tamaqe, sake miqa mata hannun tayi da niyyar tad'auketa Ko bata so, daka mata wata uwar tsawa yayi ke wuce irin marar hankalin ne? Tace bazata zoba ana dolene?"  jada baya hussentu tayi tana tsoron tayi gunguni yamaketa,
Tsaki yaja yanufii wajan diddi ya tsugunaa har k'asa yana gaidata, ta amsa masa fuska sake, tana cewa ya hanya? ya wannan y'ar fitunan? Dan yake yayi sannan yace gata nan, sai abunda yak'aru,"
Wucewa inne tayi suka bita abaya, sanda tazo dabb yanda hussentu take ta dubeta tace, kinfi karfin gaida mutane Ko?"
K'asa tayi dakanta batareda ta gaishe tanba, muryar yayanta ne yadaki dodon kunnuwanta, yace dan ubanki bazaki gaishe taba?"
Duk wata fitsarar da kikeji zansauke miki ita, jkinta har rawa yakeyi tace sannu da hanya, batareda ta kulata ba tawuce abunta, bin bayanta sukayi, har cikin gidan, da sallama suka shiga nan suka zazzauna batareda dad'ewa ba aka gabatar musu abun motsa baki,"
Hanna tagaji da zama sosai dan har dare bawanda tashigo ga k'ofa akulle, sai can hussentu tashigo, riqo hannunta tayi tace bodd'i na sannu da zama, kin gaji Ko?"
Binta da kallo kawai *hanna* tayi kwallah tafara zuba sharr a idanuwanta, mamaki ne yakama hussentu dan tunda *hanna*  tazo Ko abun kuka akayi, toh ita dariya takeyi, kamo hnnunta tayi tace yunwa kikeji?, ganin tayi shiru, yasa ta fahimcii abinci takeson tacii, futa tayi tad'auko mata kayan fruit dan tafi cinsu fiyeda komai, ta ciko plate tamm tayi d'akinta dashi, ya ishaq ne dake falo yadubii hussentu da tsawa yace ke ina zakije da wannan kayan haka d'aki, tsabar almubazzaranci, jiki na rawa tace ya ishaq zancine, c'mon wuce kiban waje, dasaurii tayi d'akinta gabanta yana fad'uwa, tana zuwa tazubewa *hanna*  agaba, tad'auka dasaurii tafara cii, shafo kanta hussentu tayi tace, kiyi hakuri nabarki da yunwa, *hanna*  batasan tanayi bama, cin abincinta kawai takeyi."

   Haka sanda sukayi  kwana biyu agidan basuga *hanna* ba, hussentu ne a d'aki tagama yiwa *hanna*  wanka tashiryata cikin, wata rigada skirt nata, wanda sunkama *hanna*  sosai, cikinta yafito dan dai-dai, tad'aura mata kwalin tayi wani irin masifar kyau sosai, dubanta tayi tace bodd'i na kinyi kyau sosai, Allah duk wanda yamiki wannan abun sai Allah ya saka miki, itakuwa *Hanna* dariya kawai takeyi sosai, fita hussentu tayi tace barina kawo miki fruit kinji, bata kulataba dariyanta kawai take zabgawa, itakuwa tasaka kai tafice."
     Ya ishaq tasamu afalo shida diddi takuama inne, sai yarinyarsa agefe tana wasa, data shige ciki ya dubeta yace, idan kinshiga ki dafawa ihsan indomie kafin kifito, toh kawai tace amma badan ranta yasoba, tafiso takaiwa *hanna* abinci, tukunna. "
   Haka tatsaya ta na yin taka tsan-tsan dan kada taje tayi wani abunda ba dai-dai ba ya jibgeta."

  *Hanna*  tazauna taga shiru, kuma gashi k'ofa abud'e, aikuwa tatashi tafito abunta, diddi na kallonta tayi saurin cewa bodd'i kona d'aki, hussentu nazuwa yanzu, itakuwa *hanna*  Ko kulata batayi ba tacigaba da k'arasowa falon,
Jin diddi nacewa bodd'i koma ciki yasa hankali inne da ishaq yayi kanta, itakuwa hussentu tafito aguje tayi wajanta, tsayqwa tayi agaban *hanna* tarufeta dake tafita tsayi, ajiye jaridan hannunsa ishaq yayi, yatshi ya nufii wajansu."
Kamar hussentu zatayi kuka tafara cewa yaya bbu abunda tamaka fa, karabu da ita, gwara ni kadakeni kaga ba lpy ne da itaba, bai kulata ba ya isa dai-dai wajansu, kuka hussentu tafashe tana yaya wallhy sai dai kadakeni, Allah kuwa bazan kauceba, sa hannu yayi ya ja hussentu tu yature gefe, numfashinsane yatsaya cakk yana k'arewa *hanna* kallo zuciyarsa tana bugawa dasaurii dasaurii, itama *hanna* ido tak'ura masa kamar maison gano wani abun, tamatso dabb dashi, tasaka hannu akan hancinsa, ai nan numfashin hussentu ya d'auke, aranta tace shikenan zai kasheta, jann hancinsa tayi ta k'arfii sanda yace auchh, itakuma tafashe da dariya sosai, tsayawa yayi yana kallonta dariyar tayi matuk'ar yimata kyau, dan gefensa ta leqa taga ihsan nawasa da teddy, dasaurii tawuceshi tak'arasa wajan ihsan, saka hannu tayi ta fauce teddy d'in, dake hannun ihsan, ihuu ihsan tafasa itakuwa *hanna* tayi saurin boye teddy din, abayanta, dasaurii hussentu tak'araso wajan takwace teddyn hannun *hanna* itakuwa *hanna* itama tafasa ihuu, tafad'ii tana shure shure, inne da ishaq harsuna had'a baki suna cewa, k'ar6aki mayar mata, wanda su kansu basusan lokacinda hakan tasu6uce abakin su ba."
    Karba hussentu tayi tamayar mata, ihsan tasa ihuu, shikuma yazo yad'auke ihsan yana cewa ki bata  Ko, zansaya miki wani."   kinjii bebyn abba, d'aga masa kai ihsan tayi, hussentu taja hannunsa *hanna* sukayi d'aki, juyawa yayi yadubi mahaifiyar sa yace diddi wacece ita?"
Girgiza kai diddi tayi tace bansantaba, zama yayi kusada diddi yace bakisanta ba kuma diddi?"
D'aga kanta tayi, sannan ta jero musu labarin had'uwwarsu da ita, dukansu tausayinta ne yakamasu, inne cikin wata sassanyar murya wanda ita kanta batasan tanada itaba balle kuma su sauran mutanen gidan tace, hafsa watanta biyu hadda satii biyu amma baku nema mata magani ba?"
Sunku yarda kai kawai diddi tayi, mamakine yakasheta duk danginsu bbu wanda yakai diddi da ishaq d'agun kai, da kuma rashin tausayi, amma kuma wai sune suke nuna tausayinsu k'arara akan *hanna*."
Abunda matukar mamaki wanda yagaza boyuwa afuskarta, ishaq ne ya nisa yace, cikinta harya fara girma, duk wanda yamata wannan abuu Allah bazai ta6a barinsaba, Ko tausayin cikin jikinta ayii abarta da hankalinta, ciki jikin mace mai baki ma ya aka kare, balle wanda bazata iya fad'in wani waje yana mata ciwo ba, yaya kenan?"
Inne ce tace, ai Allah bai bacci, Ko baka fad'i  ba, zai mata sakayya, sannan ta
Tashi tayi tace kiramun hussentu nak'ara kallonta, tashi yayi yanufii d'akin hussentu for the first time, hussentu najin sallamrsa hanjin cikinta yakad'a tatashi dasaurii, tanufo k'ofar tabud'e, kallonta yayi yace, kawota kuzo inne nakiranta, tabud'e baki zatayi magana, yayi saurin juyawa yadda bazai jita bama."

To be continued

Ur's
      Z33iiyyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

Writing by
     *©zaynab bawa*
*(Z33iiyyb3rw3r)*

_Like my page on Facebook=zaynab  BAWA novels_

 _Join my group on Facebook= ZAYNAB BAWA NOVEL'S_

   ```Ankarbo daga bban dalhata, Allah yak'ara masa yarda yace,"             Manzon Allah tsirada amincin Allah su tabbata agareshi, yanacewa,(la yadkulal mala'ikatu baitan fihi kalbun wala sura.) mala'iiuku basa shiga gidanda yakeda kare kokuma photo."```

  ================

PAGE 90

*
   Wucewa yayi yazo falon yasamu inne yace, tana zuwa sannan yajuya da ihsan ahannunsa yawuce d'aki."
   Sun kai 15minute kafin hussentu tafito hannunta riqeda na *hanna*, bata k'arasa kusada inne ba tasake ta, saka hannu inne tayi takamota, har zuwa gabanta, tanajin son yarinyar aduk wani ga6o6i najikinta,
Kallonta tatsaya yi, sannan tadubi diddi tace, asshha wannan ai yarinya ce, shakaf, hussentu ta girmeta, d'aga mata kai kawai diddi tayi, sannan tasake cewa, zan aika baban ihsan ya d'aukomin malam daga ruga, yazo yadubamin ita."
Murmushi diddi tayi kawai sannan tace Allah yakawoshi lpy, tunda dama bawai tasaba da hira da inne bane, kokad'an bataga wannan fuska ba."
   Sunyii shiru dukansu natsawon mintuna da dama, inne ta dubi diddi tace mata kuma wani irin abincii takeci?"
Mamakine yakamasu sosai, wai yau inne ce ke tambayar su, koda gaisheta sukayi saita ga damar amsawa, kokuma tad'aga kayinta kawai, diddi baki yana rawa tace, kayan itacuwa kawai tafii cii."
Koda za'ataci abincii saidai kayan zakii, duban hussentu inne tayi tace, maza tashi kije kikira sadiq yazo yak'aro mata, kayan itacuwan kada tatashi ba k'ata kuma yak'are."
Tashi hussentu tayi tanufii d'akin sadiq, tana shiga da sallama tace wai kazo injii inne, gabansa ne yayi wata mummunar fad'uwa, shidai yasan idan kaji kiran tsohuwarnan to masifa ce, jiki bbu kwari yatashi yasako rigansa sannan yabi bayan hussentu."
   Yanda isa afalo yagansu, durkusawa yayi har k'asa yana gaida ita, bawai dan yayi zaton zata amsa ba, Amma ga mamakinsa dawuri ta amsa kuma fuskarta bbu yabo, bbu fallasa,  kud'i tamiqa masa sannan tace, sadiq da'allah kaje kasiyowa yarinyarnna kayan itatuwa, karban kud'in yayi har yana had'a kafa wajan saurii mamaki, yagama kasheshi."
Baifi 40 minute ba yadawo, hannunsa d'aukeda ledoji, inne tadubi hussentu tace, karba, sannan ku daga frigde na corridor kukai d'akinki kuzuba aciki, dasaurii ta tashi, tatamakawa sadiq suka shigar da frigde d'in."   sannan tajuye kayan ledan aciki, wanda yayi saura kuma tafita dasu zuwa kitchen."

   Sosai suke kulawa da *hannna* , jinta sukeyi kamar er danginsu."
    Abuhuwa suke saya su ajiye, kozata gani tace tanaso, dan babaki take dashi ba."
     Wata ran alkhamis da safe,  ishaq yatashi yanufii ruga, yaje yad'auko malamin, zuwa 11:00.am sundawo, tareda shi, bai hutaba, yabukaci ganin marar lafiyan."
Hussentu ne taje tad'auko ta, tashigo da ita, y'an wasu addu'oii yabata, sannan yace, duk abunda yafaru sukirashi, zai zo danjin yanda jikinnata yake ahaka sukayi sallama, sadiq yamaidashi har gida."

      Yauma Marshall kamar kullum yana zaune, idanuwansa abud'e amma yanutsa cikin tunani, ummii ta dad'e akansa amma baisanda zuwanta ba, da d'an karfii Yanda zaijita, tace, yakamata karage tunani, dan zai k'ara haifar maka da wata illa ce, tashi yayi yakalleta sannan yace ummii ni tunanina d'aya yanzu awani hali take?"
  Abun damuwar kenan ummii tace, sannan tace, amma in sha Allah tana kyyyawan hannu, Allah zai bayyana mana ita aduk yanda take."
  Allah yayarda yace, sannan yakoma yakwanta, ya lumshe idanuwansa, ganin haka yasa, ummii tashi tashiga d'aki, dan tasan bawani abun zai k'ara cewa ba."
   Tana shiga saiga intisar ban, kamar kullum, tazo tazauna akujeran dake facing nasa, tagaidashi dakyar ya amsa, sannan taci gaba da zaman kuramen da takeyi kullum, sanda yqjii kiran sallah yatashi yatashi, yabarta awajen sannan itama tatashi tafice. "

     Kwance hanna take asaman carfet, ta danne cikinna ta, sosai kamar zaifashe, gashi dama cikin yafito sosai, sai murkususu takeyi, ahaka hussentu tashigo tasameta, dasaurii tak'arasa wajan ta, tana cewa haba bodd'i yanzu banhakanki kwanciya akan cikiinnan bane?"
Sokikeyi kiyiwa abunda ke cikinta illah?"  sa hannu tayi tad'agota, amma firr *hanna*  taqi d'aguwa, dan tayi nauyii cikinta yayi girma, juyawa tayi falo, tasamu, diddi tace, diddi bodd'i nanan tadanne cikinta, kuma zata iya yiwa abunda yake cikin illah, diddi tatasi tana cewa subhanallahi, kekuma baki d'agata ba?  Diddi taki nefa, d'akin diddi da hussentu suka nufa."
   Suna isa k'ofar tabud'e tashiga ihuu hussentu tasaka wanda yaja hankalin mutanen gidan, gabaki d'aya sukayi d'akin, jinine kebin *hanna*  tako ina, ta fafasa glasses ta yayyanka jikinta, dasaurii ishaq yayi kanta tana ihuu, yariqota gamm, yad'auketa yayi hanyar mota da ita, duk mutanen gidan suka wuce hospital d'in."

  Suna isa aka amsheta, treatment kawai aka mata, basu riqesuba, aka sallamosu, gida suka nufo dukansu."

  Suna isowa Kuwa kowa yabud'e yafita inne ce takamo hannun *hanna* tana cewa, zonan er albarka, mutafii d'akina yanzu, acan zakina kwana, kin koma d'akina daga yau, kallo kawai sukabii inno dashi, basu ta6a Ganin taso wani mutum kamar yanda take nuna kulawarta akan *hanna* ba."
   D'akinta tashiga da ita, tana zuwa tashiga da ita, taja hannun ta ta kwantarda ita kan bed, tana cewa, maza zonan er albarka, ki yi bacci ki huta kinjii."
  Haka tayita buubbugata kamar k'aramar yarinya har sanda tayi bacci tukunna."
  Da dare kuwa suna zaune dukansu afalo, ishaq yafito cikin shirin fita, yadubi ihsan yace, my girl zamuje anguwa ko, dasaurii ta tashi, ta nufo shii."
  Juyawa yayi yqkalli *hanna* sannan yace mata itama, zo sutafii, kallonsa *hanna* tatsayayi, galala kamar mai son gano wani abun,  hannu ya miqa mata had'eda d'aga mata kai, nan ma batasan maiyake fad'i ba."
D'an rusunawa yayi yakamo hannunta, yamiqar da ita, sannan yajuya yakalli, hussentu yace, tashi kije kid'auko mata hijab, da saurinta ta tashi, tashiga d'aki, tad'auko hijabin tazo tana k'okarin saka mata, tsayarda ita yayi yad'an rusuna, yasaukarda ihsan, yakarbi hijabin yasaka mata."
  Sannan yad'auki ihsan yajuya yakalli iyayensa yace barii mufita, kowa da Murmushi dauke fuskarta, tace adawo lpy."
    Kai tsaye wajan wani sha ice cream suka nufa, dasu duka suka shiga, amma hannunsa yana riqeda na *hanna*dan kada tayi musu barna, yasiya musu nasu itada ihsan, dakuma sauran mutanen gidan, itakuma inne fura da nono kawai yasaya mata, sannan yad'an zaga dasu suka nufii gida."
  Suna zuwa yasauke ihsan yamiqawa *hanna* robar ice cream, yawuce d'aki."
  Wajan inne taje tazauna, inne takar6i roban tasa d'an k'aramin cokalin cikin ice cream d'in, ta fara bata ahankali, tanayi tana goge mata baki, har tagama."
  Tajawota jikinta, ta kwantarda da ita akan cinyarta, tana bubbuga bayanta, jefi-jefi kuma suna hira, wanda hakan yafaru ne ad'an kwanakinnan, nazuwan *hanna*  har inne kesakewa tana hirada su."


   Haka sukaci gaba da kulawa da *hanna*  sosai har cikin ta yakai 7month, tacika 6month da 6acewa kenan, yanzu yakasance awannan dangi bbu maijin haushin wani kokuma wani yak'i kula d'an uwansa hira sukeyi sosai, ta shiga ransu, itama Kuwa tasaba dasu sosai."
   Dan koda batasan mai suke fad'aba idan sukayi magana tasheke da dariya suma Haka zasu bita suyita dariyan."
 Wani lokaci kuma idan anyii magana sai ta amsa da kayi kamar wanda tajii mai suka fad'a."
   Kuma alamun ma yanuna cewa ta fahimta."

To be continued

Ur's

      Z33iiyyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

Writing by
     *©zaynab bawa*
*(Z33iiyyb3rw3r)*

_Like my page on Facebook=zaynab  BAWA novels_

 _Join my group on Facebook= ZAYNAB BAWA NOVEL'S_

.

================

  Page 91

*
   Labba ce zaune sai dube-dube takeyi, Marshall dake kusa da ita, duk tabi tadameshi, da k'aran paper's, tsaki yaja yadubeta yace, wai mekike nemane?"
   Bata d'ago ba tace wallhy yaya wai takardan asibiti na affan ne da anty afeeya tazota ta manta, zasu koma ne, tsaki yaja kawai yatashi, yashige d'akin ummii nan ma ganii yayi tafito da takrdu duk ak'asa, tsaki yaja yakwanta akan bed, ya lumshe idanuwansa shi dai ba bacci yakeyibaa."
  Juyi yayi idanuwansa sukakai kan takardar dake cikin paper's data futo dasu, ganin anrubuta Aminu kano hospital, yasa yayi tunani Ko itace takardan, kamar wanda baiso yakira Labba, Labba, amma bata amsaba, dan baiyi maganar yanda zatajishi bama, ganin Ko kad'an batajii ba, dama kuma bawai yayi maganar yadda zataji bane, tsaki yaja akaro bila adadin, yatashi yak'arasa har gaban takardan yasaka hannu yad'auka."
Fita yayi zuwa falo batareda yadubaba ya miqa mata yajuya, k'arban takardar tayi tafara dubawa, zaro ido tayi, arazane tace yaya, tsayawa yayi batareda da juyo ba, bata damu da hakanba, tak'ara cewa yaya, wannan takardan *hanna*  nefa, dasaurii yajuyo tacigaba dacewa, kuma yaya gani nayi kamar takardan da take nuna tana d'auke da cik,,,, bata k'arasaba yayi saurin karasowa yafauce takardan, ahannunta, kafin en secouns idanuwansa sun kad'a sunyii jajirr, idan ba idanuwansa gizo suke masa ba, gani yayi kamar takardan tana nuna *hanna*  nad'aukeda ciki na 1month ba kenan, dasaurii yafice da takardan ahannunsa yanufii shahsin mai martaba."
  Afalo yasamu ummii ta abbansa suna zaune, Ko k'arasawa bai iyayiba, zuciyarsa na masa k'una yace, ummii yanzu dama *hanna*  nad'aukeda ciki baki gayamun ba, ummii menene amfanin b'oyemun dakikayi, alhali kinsan duk daran dad'ewa zan sani."   bai kara cewa komai ba yajuya  yafice, ummii tatashi dasaurii zata bishi mai martaba yayi saurin tsaida ita yace, rabuu dashi, kada kije kusadashi, dan yanzu yana cikin zafin zuciya, abun yaronnan  yafarayin yawa, narasa maiyasa yakasa d'aukan k'addara, komawa ummii tayi ta zauna, tausayin d'anta fall aranta, dubanta mai martaba yayi yace, toke menene dalilinki na b'oye masa matarsa tanada juna biyu?"
Dakyar ummii ta iya cewa ina tunanin halinda zai shigane idan yasanii, damuwar sa ta yanzu zatafii tadah.  Niasawa mai martaba yayi, yana tausayin kansu dan dukansu abun rausayine, yana tausayin *hanna* Ko yanzu wani hali take da juna biyu."
  D'aga hannu mai martaba yayi sama yace ya Allah kaga irin jarabawar da ka jarbci bayinka dasu, Allah ina roqonka da ka bayyana mana wannan yarinya, Allah kakare baiwarka cikin kowani irin hali take."  Allah kasada ta akykkyawan hannu. Amin ummii ta amsa dashi."


   Marshall yana fita shahainsu yawuce kai tsaye, mukarrabansa na biyedashi abaya, shahin yayi k'ura sosai tunda *hanna* ta6ata bbu wanda yak'ara shigansa."
  Zama yayi akan carfet dirsham bai damu da dattinsa ba yace, hava *hanna*  yaya zakimun haka?"  mena miki haka, zataki tafii kibar zuciya ta cikin kunci? ashe duk maganganun da kike fad'a da gaskene? ashe dama tafiya zakiyi ki barni yasa kike fad'amun irin wannan maganar?
  Hawaye ne yabiyo kuncinsa, wanda rabonsa dasu tun yana yaro, yana yaronma bazai iya recalling lokacin ba."
Baidamu daya goge hawayen ba, dan koya goge wasu zasu biyo baya, kuma aganinsa hawayen dake zuba a idanuwansa, sune sassauci agareshi, zaiso sufii haka yawa ma, zaiso ace yayita kuka, har indai hakanne zaisama masa sauki,
Lokacii d'aya kansa yasara yahau ciwo, cikin ransa yana tunani yanzu awani hali, *hanna* ke ciki da juna biyu."
Sunbatu kawai yafarayi,
Hawayen na zuba yak'ara cewa meyasa zakimun haka, kinyi alqawari bazaki bazaki fad'amun irin magan ganunda ke sani cikin damuwa ba, balle yaje ga tafiya ki barni."
Yanda kasan wani zaucecce yaketa maganganu , wasun kanma koya fad'i bazaka gane meyake nufii ba."

  Marshall yakai 3day's bbu wanda yakalli kwayar idanuwansa, yana cikin shashinsu, koda anzo ana bugawa baya kula kowa, yanaji yake sharewa, mai martaba yakira baba yasanarda shi abunda ake ciki."
Sosai baba yaji bbu dad'i aranar yakamo hanya yazo garin, yana isa ya wuce fada, dake shikad'ai yazo Ko driver bai d'auko ba."
 Sosai mai martaba yaji dad'in ganinsa, bayan sun gaisa ne mai martaba yasa aka kira masa ummii, takai 15minute kafin ta iso, duk tarame gabaki d'aya ta lalalce, bayan sun gaisa ne, baba yad'an nisa kafin yace, shawara ce nakawo, wanda ina tunanin shine mafita dashi damu kuma baki d'aya, mai martaba ne yace, muna jinka, dan yanzu dolen mafita muka zauna nema, baba yacigaba da cewa, ni aganina abunda zai zama maslaha damu dakuma yaronnan shine kawai, ak'ara masa aure, gaban ummii ne yayi wani mummunan fad'uwa, tace haba da Allah, wai ce muku akayi *hanna*  baxata dawo bane Ko kuma?"  girgiza kai kawai baba yayi yace Ko d'aya ba'ace *hanna*  bazata dawoba, kuma shi ai mijin mace hud'u ne, koda tadawo saidai tayi hak'uri, amma Ganin wata kusada shi zai rage masa damuwa,zai rage yazauna yana tunani, mai martaba baice komai ba juya maganar kawai yakeyi, sai dayaji kowa yayi shiru sannan yace, amma kana ganin hakan shine mafita bbu wata hanya? Girgiza kai baba yayi sannan yace gaskiya idanma da'akwai wata hanyar nidai  bansanta ba."
  Mai martaba yace, toh Allah yaza6ar mana mafii alkairi, da ameen baba ya amsa, sannna yacigaba da cewa, baka ganin er k'aninka, naga kusan kamarsu d'aya da ita *hanna*  d'in ai sai ka tambaya masa ita, dasaurii ummii tacafe, tace wah wai hameeda kuke nufii, amma wannan babban cin amana ne, er uwartata xaku aurawa mijinta dan bbu idonta, wallhy Allah bada yawuna za'ayi wannan auranba, tatashi tafice tana sharar kwalla."
  Binta da kallo sukayi su dukansu, sannan mai martaba yace, kasan halin mata da wani irin abuu, abunda Allah ya halasta su zasu nemi haramta maka shii."
   Nan sukayi sallama suka tashi akan baba zai wuce su zauna suji yadda za'ayi shida, abba."

  Umma nashiga d'aki tafashe da kuka, kawai tana jajanta abunda ake shirin aikatawa baiwar Allah."

  Labba ne tamatso kusada ita tace, ummii menene yafaru?"
  Wani abunne yasamu yayan?"
Girgiza mata kai ummii tayi, sauke ajiyar zuciya Labba tayi, ummii ne tace kayya er nan daina wata ajiyar zuciya ina maraban wani abu yasameshi, da abunda ake shirin aikata masa yanzu."
  Riqo hannun ummii Labba tayi tana zazzaro ido sannan tace, me za'ayi masa?"
Aure zasu masa, ummii tabata amsa atakaice, aure kuma ummii?"
Eh aure kuma wai er uwarta hameeda, subhanallahi hameeda ummii?"  wannan wani irin cin amana ne, nan danan idanuwanta suka fara zubda kwalla."
  Tatashi dasaurii tafice dagudu, bata tsaya ba sai sashinsa, tana zuwa tafara bugawa kamar wata mahaukaciya, jin bugun yayi yawa yasa yatashi, dakyar yabud'e, kofan."
   Dagudu Labba tashige jikinsa tana kuka, bubbuga bayanta yafarayi, amma bai iya magana ba, sanda tagaji dan kanta tad'ago tadubeshi tace, yaya Allah aure zasu maka, suwa? ya tambaya, su abba, mana, d'agota yayi yace kai Labba kodai bakiji dakyau bane?" ni nace musu inason aure?"  Allah kuwa yaya wai kuma da hameeda, zaro ido yayi yace hameeda kuma labba, eh Allah yaya, ajiyar zuciya yasauk'e yace to ai yazo gidan sauki, zuwa gobe, zanshawo kan matsalar har indai hameeda ce, dawatace sai in damu."
  D'agowa tayi tadubeshi tace Allah yaya, d'aga mata kai yayi yace, Allah kuwa acikin week d'innan zan shawo komai."
  Sai alokacin hankalin Labba yad'an kwanta, tadubeshi tace yaya kaci abincii ne, girgiza kai yayi yace banjin yunwa ne, yakamata kaci ai tabashi amsa takaice."
  Tashiga kitchen tahad'a masa abincii, dakyar yaci, sanda yaci kuwa tabar shashin, taje tafad'awa ummii Yanda sukayi, Allah yasa adace kawai ummii tace."

    Baba ya isa gidan abba suka zauna, sukayi magana, abba fur yak'ii yarda, sanda baba ya nuna masa bacin rai, ya ce, idan kanaso kanunamin bani nahaifeta ba shikenan, amma ni nadauka yarana da naka duk d'aya ne, nan danan abba yarikice, har idanuwansa suka ciko yace haba yaya, wannan wani irin magana ce, baba ne yace idan bahaka kake nufii ba, mai yasa zanyi magana kace bahaka ba."
  Kayi hak'uri yaya wallhy hameeda erka ce duk Yanda kakeso kayida ita."
Tom nagode idan kashiga kayiwa matarka magana kajii, nima idannaje zanmata magana."
  Ahaka sukayi sallama."
Abba ya tashi yashiga gida jikinsa bbu kwarii."

To be continued

Ur's
     Z33iiyyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

Writing by
     *©zaynab bawa*
*(Z33iiyyb3rw3r)*

_Like my page on Facebook=zaynab  BAWA novels_

 _Join my group on Facebook= ZAYNAB BAWA NOVEL'S_

    ```Alhmdllh am so much bless, addu'anku sunyi aiki, godiya Mai yawa```

================

PAGE 92

  *
Yau ma kamar wancan karon sassafe sadiq yatashi yatafi ruga d'an d'auko malam,
Dake malam baisanda zuwansa ba, kuma baishirya ba, sanda yajirashi ya shirya, sai 1:00.suka iso, yana zuwa yabaukaci ganin *hanna*, kawota akayi sai zazzare idanuwanta takeyi kamar wanda tayi k'arya, dasaurinta tak'arasa gefen inne tazauna."
   Cikin damuwa inne tafara yimasa magana, tace, malam duk randa nabata ruwan addu'oii nan, saitayi k'ok'arin halaka kanta kokuma abunda yake cikinta, kuma tanashan wuya sosai."
   Malam ayad'anyi shiru kafin yace, maganar gaskiya yarinyarnna turan aljanu aka mata, kuma ahalin yanzu idan aka matsa sai anciresu, kafin su fita zasu cutarda ita kokuma abunda yake cikin ta, zasu iyayin sqnadiyar cikin, idon inne ya cikciko tace yanzu wannan yarinya wani abu zatayi dahar za'a tura mata aljanu, mutane kokad'an bbu imani."
   Malam ne yadanyi jim kafin yace, Aibasai tayi musu wani abunba, yanzu d'an adam ake kiwo, ba dabba ba."
  Yanzu  nakaoma zanyita yi mata addu'a da sauk'an qur'ani, yanzu zaikai kaman yaushe haihuwanta?"
 Diddi ne tace, ba lallai ya k'arasa nanda wata biyu ba."
Toh in sha Allah nan da wata biyu zata samu sauki, dan yanzu Allah kad'ai yasan halinda danginta suke ciki."
   Jijjiga kai inne tayi tace, hakane dole zuri'arta zasu kasance cikin tashin hankali da zullumii."
  Allah yabata lpy, dukansu suka amsa da amin, sai bayan la'asar, sadiq yamayar da malam."

    Marshall ne zaune da kayan soldier's, ajikinsa rabonsa da saka kayan yakai 7month, yarame kam sosai, amma Sun masa kyau sosai, wayansa yad'auko yayi dialing numb d'in, captain Ahmad wanda ayanzu yadawo genaral Ahmad, yana shiga kuma aka d'auka, baijira wani sabon zance ba, yace kasameni a shahi na."
  Kusan 30minute kafin yak'araso sanda yakirashi yanemi izinin, shiga kafin yashigo, ganin agonnasa ayanayin daya dad'e bai ganshi ba yasa yak'araso dasaurii, yana fara'a, wajan zama yabashi, sannan yace magana nakeson muyida kai sannan kuma, ina neman alfarma, dasaurii, G Ahmad yace hava, yallabai yanzu har zaka nemi abuu awajena, sai ka kirashi da, taimako, kafadeshi kawai kai tsaye amtsayin umarni, Murmushi Marshall yayi sannan yace, yanzu zaka goyi bayan nayi aure?"
  Aure kuma yallabai kokadan bazan goyi baya ba."
  B'atan madam ba hakan yana nufin bazata dawo bane, wallhy yallabai Ko 10yrs zatayi kajirata, dannasan idan itane awajanta, itama jiranka zatayi."
  Yak'e Marshall yayi akaro na biyu sannan yace, kuma er uwarta sukeso na aura, girgiza kai G Ahmad yayi yace, gaskiya hakan baidace ba,
Jijjiga kai Marshall yayi yace shiyasa nakeson kataimaka mun yau daddare kaje gidansu amatsayin, kana sonta, banso kab'oye mata komai, inason kaida ita, ku nunawa iyayenmu kun dad'e kuna soyyaya, dannasan nata wajanma bayarda zatayi ba, idan kaje mata da wannan maganar zatayi saurin amince wa."
   G Ahmad ne yace indai hakan zaitaimaka, to nayarda zan aureta, zanje yau nasameta, nagode Marshall yace, Ahmad ya girgiza kai yace bbu godiya atsakanina dakai."
  Ya tashi yafita."
Dad'i ne yakama Marshall nafarko yarabu da aurenda akeso ayi masa, nabiyu kuma, na cikawa *hanna* burinta, dan bai manta lokacinda tace masa, inason kacikamun burina kasa, C. Ahmad ya auri hameeda."
  Tashi yayi fuskarsa ad'an sake yanufii sashin mahaifinsa."
  Su kansu sojojin sa sunyi mamaki, yanda yau suka ganshi, yana cikin kuzarinsa, da sallama yashiga, falon mahaifinnasa, amsawa mai martaba yayi dan ya dad'e baiji shi da irin wannan muryar ba."
Koda zaiyi sallama saidai yayi ciki-ciki, kallonsa mai martaba yakeyi, har yak'arasa shigowa,
Yazauna yana gaidashi, shi kansa yaga fara'a kwance fuskar mahaifinsa, alamun yaji dad'in ganinsa ahaka."
  Mai martaba ne yacigaba da cewa, dama gashi inason muyi magana, sosa kai Marshall yayi yace to ai gani abba."
   Gyaran murya mai martaba yayi yace, dama inason na fad'a maka munyanke shawrar yimaka aurene, zaro ido yayi, sannan yayi kamar baisaniba yace, aure kuma abba, eh aure tunda kakasa daukan qaddara, kuma er uwar matarka zan aura maka, wacce kenan abba?, er gidan k'aninsa, kamar da gaske Marshall ya nuna firgici yace, abba budurwar Ahmad nefa, wani Ahmad? Dan gidan kanwan ummii mana, abba shine saurayinta, yaya za'ayi haka,  k'anina nefa kamar yanda nakejin affan haka nake jinsa, kuma ku kad'ai yasani matsayin iyayensa, zai d'aukeku masu sonkai idan kukayi haka."

   Shiru mai martaba yayi duk jikinsa, yayi sanyii, yadubi Marshall yace tashi kaje, zankira Ahmad d'in zanji tabakinsa zansame ka."

  Tashi yayi yamiqe yafice murna aransa fall, yayi nasara danya fahimci jikin abba yayi sanyii."

  Abba ne yashigo afalo yasamu umma, badai yadda take walwala ada ba, zama yayi kusada ita yace khadija, juyowa tayi takalleshi, yace inaso muyi magana, amma kuma yakamata ki fahimceni, yakamata ki fahimci mezan fad'a miki, dan kada kiyi mana gurguwar fahimta, kisani komai mukaddarine daga Allah, nan yafara zayyano mata bayani, kallonsa kawai umma takeyi, ji takeyi, kamar tashaqe shi kokuma tarufeshi da duka, juyarda kai tayi gefe, har yagama bayanansa ya wuce, tabishi da kallon banza kawai dan wani haushi yabata."

Tashi tayi tanufii d'akin hameeda, tana zuwa taganta kwance akan gado, duka ta d'aka mata, wanda yasa hameeda zabura tatashi, tana shirin kurma ihu."
Umma tace da Allah rufamin baki, nasan abbanku zuwa jmawa zaizo miki da maganar wai zasu aura miki mijin er uwarki, idan kika kuskura kika amince nidake, zaro ido hameeda tayi, sannan tace umma er uwata kuma wacce?"  mijin *hanna* zasu aure miki, wallhy idan kika amince saina kasheki, kuka hameeda tafashe dashi, tace haba umma yaya za'ayi na'amince, kamar uwa d'aya uba d'aya fa muke, kima amince dan wallhy zan iya kasheki, kokuma in tsine miki, kuka takeyi tana cewa wallhy bazan amince ba umma."
   Rufo mata k'ofar tayi da karfii, itakuma takoma takwanta tacigaba da kuka." jitakeyi kamar amafarki wai mijin *hanna*,
 

  K'arfe takwas dai-dai mai gadi yashigo afalo yasamu umma yagaidata, sannan yace, hajiya wani yana sallama da hajiya hameeda, ak'ofar gida, umma ne tace jeka kace tana zuwa, leqa d'akin hameeda tayi taganta tanata kuka kamar ranta zai fice, bak'in cikinta d'aya wai arasa wanda za'ace ta aura sai mijin er uwarta."

  Kitashi kije ana sallama dake awaje, mamakine yakama hameeda ganin, Ko ance ana sallama da ita umma sai tace ace batanan."
  Yau itada kanta take cemata tajeta ana kiran ta, harta juya zata fita sai tace, yauwa sannan ki gyara fuskarki, ki tareshi da tad'i, har babanku yazo yasameki."
D'aga kanta kawai hameeda tayi, sannan tatashi tashafa powder, da turare tasaka hijabinta tafito fargabanta d'aya Ko waye yazo wajanta, itadai data aurii mijin *hanna*  gwamma koma waye ta aura, afalo tahad'u ta umma, har tawuceta tajii umma nacewa, kuma kada kiga nace kifita kije kiyi rawar kai, ki kulada mtumcinki, kisan cewa Allah yana ganin ki, d'aga kanta kawai tayi tafice."

   Ajikin mota tasameshi yana jingineda mota, tun kafin tak'arasa tagane wanene."
  Tana isa tagaida shi, ya amsa, bai boye mata komai ba yafad'a mata yanda sukayi da Marshall, Jijjiga kai tayi tace wallhy hakan yafii, bansan wani irin abuu sukeson aikatawa ba."
   Kallon fuskarta yayi yace, kin amince dani kenan, kai kawai tad'aga masa, nan ya bata labarin sa, har tad'an saki jiki dashi suna hira."
   Motan abbane tadanno kai, tun daga nesa yahangeta tana hira, bai kulata ba yayi saurin parking Motan ya fito ya shigewa gida."
  Anan falon yasamu ummii, zama yayi cikin sanyin jiki yace wai baki fad'awa hameeda wannan maganar bane naganta atsaye tana hira, umma ne tace, banfad'a mata ba, tunda naga tanada wanda takeso, kulllum yana zuwa hira nayau d'aya ace anmata miji, dawuya ace na fad'a mata wannan zance lokaci d'aya sai dai idan kai zaka fad'a mata idanta shigo."

   Ganin lokaci yaja g Ahmad yace, barin tafii time yanaja sai gobe zanzo, kai tad'aga masa, sannan yace kuma kada kisake yin kuka anshawo kan matsalar dan fuskarki tanuna kinyi kuka, bazan sake ba tace sukayi exchange na number, sannan sukayi sallama."

   Afalo tasamu abba gabanta yayi mugun fad'uwa naganin sa, amma tadake tace sannu da dawowa abba, yawwa sannu yace, tana k'okarin wucewa, yace dawo nan zamuyi magana dake, dawowa tayi tazauna yadubeta yace, waye wannan wanda naganshi tareda ke yanzu, sunna kai tayi kamar maijin kunya tace, abba k'anin mijin *hanna*  ne, shima sojane yanzu yakai matakin general, gaban abbane yafad'i, ya k'ara maimaita k'anin mijinta kuma, tace eh, yace Yau yafara zuwa kenan, girgiza kai tayi tace, A'a abba tun bikin *hanna*  muka had'u baku ta6a had'uwa bane."
  Yadad'e ma yana cewa zai turo banbashi dama bane."
  Abba bai iya cewa komai ba yace tashi kitafii, tashi tayi tamiqe, dad'ii yacikata ganin yanda jikin abba yayi sanyii."

   To be continued

Ur's
      Z33iiyyb3rw3r

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *