Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, August 26, 2019

Bugun Zuciya Complete Hausa Novel

adsense here
Bugun Zuciya Complete Hausa Novel
Compiled by Umar Dalha.




 💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
   ( _Heartbeat_)

                   💓💝💗
                        💗           

💓💝💗
*By*
     💗
    _*Fadeela Lamido*_

       
        1⃣ to 3⃣


*Dasunan Allah Mai Rahama maijin kyai*




📙 Dada! Dada!! Wata matashiyar yariya ce ke rangadawa tsohuwar kakanta kira"

    Fitowa tsohowar tayi tana kokarin gyara daurin zaninta take fadin, nashige su nikam wannan irin kira haka?"



    Turbune fuska yariyar tayi lokacin da sukayi ido biyu da kakar tata tana fadin ayya dada danma kinsamu ina murnan ganinki shine zakice wani kin shigesu?, juyawa tayi da nufin komawa, cikin sauri dada ta jawota cikin fara'a tace dawo2 ai ban dauki murya ba, maraba lale lale takwara, karashewa tayi tare da jawota jikinta ta rungume"

     Daidai lokacin wani farin dattiju ya shigo tare da sallama, yana ganin su haka yasaki murmushi"

    Cikin sauri yariyar ta kwace daga rukon dada ta nufi cikin dakin, tabarma ta dauko ta shinfida wa mahaifinta ya zauna tana jin sun shiga gaisawa da dada ta koma dakin dada"

    Gyarawa tashigayi duk da cewa dakin agyare yake dan dada macece me matukar tsafta, gadon ta lokuikuye yayi tsaf kaman baza ahauba sannan ta dau tsintsiya tahau shara"

    Bayan ta gama ne ta dauko dan kaskon turaren wuta ta nufin dan karamin kitchen din dada dake tsakar gida"

     Tagabansu dada tazo zata wuce dan haka duk suka juyo suna kallonta harta kusa isa kitchen din dada tace"

    Aiko takwara bazaki samu rushi a kitchen dinnan ba, dan yanzun baban ninki sun hanani amfani da murhu"

    Juyowa tayi ahankali tace to yanzun baki kunne turaran rushi kenan?

    Gurin tabawa nake samowa"

    Cikin rawar jiki ta nufi kofar gida tana fadin bari naje na samo"

   Lokacin da dada ta komar da kallonta ga dannata gani tayi yayi shiru kanshi akasa, gyaran murya tayi sannan tace girman dan mutum babu wuya yanzun dan Allah kalli yadda takwara ta girma ko yanzun aka mata aure saita xauna"

    Da sauri ya dago kai, yace dada kin sosamin inda ke min kyaikayi, hankalina ya fara tashi ayau tum muna hanya zuciyata ta fara tsinkewa"

   Cikin kulawa tace kakwatar da hankalin ka insha Allahu Allah zai tsare babu abin da zai faru, kuma ma ai takwarar tawa Allahamdulillahi natse take tsaf ga kunya ga tsafta"


     Hmmm dada akwai wani hali dana kula tanashi wadda har yanzun banji kowa ya furta ba, ban saniba koni kadai nake gani?

   Kaga, banason jajibe2 karkace komai tunda ta gama secondary data same miji amata aure, idan ma kana da burin tayi karatu ne idan tayi aure tayishi can dakin mijinta"

   Nisawa yayi daidai lokacin ta shigo da sauri tashige dakin dada cikin kankanin lokaci kamshi ya cikka gidan"

    Dada ko hira sukaci gaba da danta zuwa can ya dauki mukullin motar sa dake kan tabarma yayiwa dada sallama ya fice"

    Mikewa dada tayi ta nufi daki tana fadin takwara maza ki fito kutafi kisan abbanki besan jira"

    Aguje ta fito ranta bace ta kalli kakar tata tace kai dada memakon kice mishi yabarni anan, ninafi son zamagurin ki kuma, shiru tayi kawai ta nufu kofa cikin zubura baki"

    Binta da kallo dada tayi harta kule, sannan ta sauke idananunta tare da fadin duk sanki da gidan nan *Asma'u* dole ki hakura dan babanninki ba yadda zasuyi ba"

    Ko da suka kama hanya babu abinda take banda zunbura baki, abbanta na kula da ita saidai ya dauke idon daga kallon ta dan ya fahimce manufarta"

    Suna isa gida ta nufin dakin mahaifiyarta ranta bace, tare da matso hawaye"

    *Ma'u* ya, kin fita da farinciki kuma kin dawo min da kuka, menene ya faru?

    Turo baki ta karayi cikin kuka tace mama nifah banason gidan nan nafison gidan dada, kuma aidama keda abba kuncemin idan na kare secondary zan koma can"

    Shiru mama tayi tana nazari kafin ta dago kai abba yayi sallama ya shigo ganin su haka yasashi hade fuska tare da fadin yaya ne?

   Mikewa mama tayi tare da fadin alhaji ai kafi kowa sanin halinta gatanan wai ita gidan hajiya takeson zama"

   Bazaiyuwu ba mamana, idan kikayi wasa konan da kofar gida zan hanaki fita, kinga yau kika dawo daga makaranta karki yadda wani abu ya hadani dake ban ce bazaki koma gurin dada ba, amman sai naga yanayin natsuwar ki, yana gama fadin haka ya fice abinsa ko waiwaye babu"

   Washegari


  *Asma'u* ce tsaye gaban mama cikin shirinta na tafiya islamiyya jan wando farar riga tare da jan hijjabi kudin break mama ta miko mata sannan ta mata sallam ta fice"

   Gidan kawarta Zainab ta nufa cikin sauri dan karta wuce ta barta"

     Tana kokarin shiga gidan zainab na fitowa cikin farin ciki suka rungumi juna cikin dauki zaina ke tambayan ta yaushe kika dawo?

   Jiya abba ya dauko ni, jawo hannunta tayi tana fadin zo mutafi idan mundawo mayi hirar danni tsoron bulalan baba idi nake"

    Mike layin sukayi har sun kusa isa makarantar zainab tajawo hannun *Ma'u* tanufi wani dan lungu"

    Cijewa *ma'u* tayi tare da fadin me zamuyi alungu kuma?

    Cikin rawar jiki tace *ma'u* taho dan Allah kinga waccen, na zaune din cen, dan daba ne idan yana zaune agurin ko maza basa wucewa, kizo mu wuce tunkan ya hangu mu"

    Hannu *ma'u* ta daga ta nunashi tare da ya tsuna baki tana fadin waccen din?

     Bege hannunta xainab tayi tace ke *ma'u* wlh idan yaga kina nunashi munshiga uku, gudun tsiya ne dashi kuma jikin shi duk wukake ne, ranan fa muna aji muna karatu saiga baba idi aguje, sai haki yake wai duna ne ya biyoshi"

     Tintsirewa *ma'u* tayi da dariya hartana rike ciki, ganin haka yasa Zainab ta sake ta arude takoma jikin wani gida ta labe"

    Tsagaitawa tayi da dariyar sannan tabi bayan zainab kallonta tayi tace gaskiya ke muguwar matsoraciya ce nikam bebani tsoro ba, dan haka wlh ta gabanshi zan wuce, ai layin bana ubanshi bane dazai hana mutane wucewa dallah fito mutafi"

       Fitowa zainab tayi daga mabuyarta tana share zufah, dariya *ma'u* ta kara tutsirewa dashi sannan ta kama hannun zainab tana fadin to meyasa akecemishi *Duna* kuma gashi ba baki bane?

   Oho nima haka naji anacemai *Shamsu duna* tafiya suka fara dan haka kowaccen su ta tsuke bakinta"

     Lokacin dasuka isa dafdashi zainab ta sunkuyar da kanta kasa tare da sauri, itako *ma'u* kur tamai da ido tana karemai kallo,
dan haka zainab ta
Wuce tabarta agurin"

      Zaune yake idon shi akasa yana wasa wuka, dogo ne kakkaura bashi da haske kuma baza akirashi baki ba, gabobinshi abon tsoro ne duk sunbi sun murmurde xaikai kimanin shekara 33 zuwa da 35, tabone ajikin shi kaca2 gani tayi yana kokarin dagowa dan haka ta fara kokarin dauke kanta dai batakai ga dauke kan nataba suyi ido 4"

    Tsoro ne ya kamata sosai cikin sauri ta kalli kofar makarantar  gani tayi har ankulle wani sabon tsoron ne ya sake kamata, batai aune ba saiganin *Duna* tayi agabanta"

  Kerma ta fara dare da kara kallon wukar dake hannunta sai kyalli take, ahankali taxame tasa gwuiwanta akasa cikin rawan baki tace * yaya shamsuddeen inakwana?

   Hadiye wulakancin daya tanazo yayi tare da tsareta da ido"

    Cikin daure fuska yace mike"

 Da saurinta ta mike tana kokarin wucewa"

   Zonan taji ya fada dawowa tayi ta tsaya tare da runtse ido dan tunda ya matso kusa da ita tagane jikinshi abun tsoro ne gashi babu rigar kirki ajikin shi"

   Ta dade ahaka ganin da tayi baya da niyan mgn yasata bude idonta, mamaki ne ya kamata dumin hangoshi tayi ya koma gurin zaman shi idon shi lumshe kaman me bacci

    Aguje ta karasa makaranta jikinta sai rawa yake, abakin gert din ta tsaya ta saita kanta sannan ta karasa cikin mkrntr, office din baba idi ta kalla tare da addu'a Allah yasa baya ciki dan tana masifan tsoron dorinar shi, tsuguna wa tayi ta cire takalmanta ta fara takawa ahankali sadaf2 harta wuce office din tashege ajinsu"

     Saidai duk abinda take baba idi nadaga can gefe yana kallon ta hannun shi rike da buta dan yagama alwala kenan ya mike ya hangota tana sanda"

    Kai ya girgiza sannan ya shiga tunani yariyar nan batajin mgn duk da cewa mahaifinta namatukar kokari wajen bata tarbiya, dukanta yaso yi sai dai yasan halin *Asma'u* da tsoron duka dan ta makalkaleshi bawani abu bane awajenta, dan haka gara kawai ya barta"

   Karfe 11:30am aka tashesu sai dai ana buga kararrawan baba idin ya aiko akira masa *ma'u*

    Hankalinta be tashiba kawayenta taja su uku suka isa gurin baba idi"

    Hango fuskanshi kawai sukayi su kasan lallai babu wasa dan haka duk suka doje"

    Haushi sosai *ma'u* taji ahankali ta fara takawa harta isa gabanshi"

     Cikin girmamawa ta gaidashi sannan ta sunkuyar da kanta kasa"

    Ke *Asma'u* karfe nawa kikazo makaranta?

     yau?

Kinci gidan Ku, ai Ina kallon ki sanda kikazo, meya yahana ki zowa makaranta akan lokaci?

     Um um baba wlh daman yaune abban mu ya daukoni daga makaranta yanzun fah ko gida banje ba......

  Sakin baki baba idi yayi yana kallota yarasa ma me zaice mata shiru yayi yana kallon kasa zuwa can ya dago yace"

    *Asma'u* yau yaushe?


      Alhamis"

   Cikin ido baba idi ya kalleta

     Ganin haka *ma'u* ta fara girgiza jiki alman tsoro, runtse ido baba idi yayi domin gani yayi kirjinta na tsalle, addi'oi neman tsari yayi sannan ya bude ido yace"

    *Asma'u* ? Ki kace yau alhamis?

     Shiru tayi dan haka ya girgizakai sannan yace Allah ya shirye ki"

Harta fara tafiya taji muryan shi yana cewa, ai zanga baban naki"

     Tsurrr cikinta ya kada, cikin sauri ta juyo ta tsuguna tare da fadin me kace?

   Jeki kawai ba dake nake ba"

    Marai2 cewa tayi idonta cike da hawaye tace baba dan Allah karka gayawa abba wlh daga yau nabari"

    Shiru kawai yayi yana kallonta dan becika son yin dogowar magana da itaba duk da yariya ce karama tana matukar birge shi saboda saurin kadaukan karatu da anbiya data dauke shi, kiriniyarta kawai ke hada shi da da ita domin duk fadin makaranta bawanda besan da zaman *ma'u* ba sabo da tsokanar tsiya"

     Kara daure fuska yayi sannan yace naji tafi"

    Jikinta asanyaye ta isa gurin kawayen ta dasukayi tsaye bakin mkrntr suna jiran ta, dan duk daliban sun wuce suka dai suka rage"

    Tana shiga cikin su ta manta da zancen wani baba idi, lbrn haduwanta da *Duna* ta fara basu"

     Rahama da faty ne sukaita kwasan dariya dasukaji *ma'u* ta tsugu ta gaida *Duna* itako zainab kara rudewa tayi cikin sauri ta nufa lungun da taso bi dazon tana fadin nidai saikun taho"

     Basu hanataba tafiya suka fara suna cigaba da zancen *Duna*"

    Rahama wai meyasa ake cemishi *Duna*?, ni naga beyi bakin da za'ace mishi haka ba, ni fuskar shi wlh kyau tamin jikinshi ne kawai yabani tsoro"

    Au ke har kallon faskan tashi kikayi ni bantaba mai kallon kurullah ba dan baya son a kalleshi, amman naji mutane na cewa wai *karan* shi ne bakinkirin shiyasa ake kiransa *Shamsu duna*"

    Hannun Rahama ta rike sannan tace toh wai meyasa baya son akalleshi?

    Oho nima bansani ba"

    Faty ce takalli *ma'u* tace kefa kin cika tambayan tsiya idan kin matso kije ki tambaye shi"

  Murmushi kawai *ma'u* tayi, shiru sukayi harsuka isa gurin da ta ganshi daxun sai dai yanxun babu kowa agurin, raba ido *ma'u* tafara duk ta waiga babu alamansa, cizon yatsa tayi  sannan tacigaba da tafiya

    sun wuce gurin da kadan suka hango shi jingine jikin wani gida ya rufe fuskan shi da hula, da alama bacci yake"

    Cikin sandan suka wuce shi, ja *ma'u* tayi da baya tare da fadin kash😬 na manta xobe na aji kuxo ku rakani na dauko"

    Faty ce ta bata fuska sannan tace gsky kibari da yamma kyaduba"

    Sakin hannun Rahama *ma'u* tayi sannan tace kuje sai nazo dan bazan iya zuwa gida babushi ba, abba na ne fah ya sayomin shi a Dubai"

     Da haka tamusu wayo ta koma baya sai da ta bari su Rahama suka bace da ganin ta sannan ta tsuna ta debi dutsinan ta madaidaita guda 3  a hankali take takawa  jikin gidan dake kallon shi ta nufa ta shige dan wani lungu dake tsakanin gidajen guda 2 ta labe, dutsen ta daya ta dauka sannan tayi saitin *Duna*



   


    _Heartbeat_
*Mmn Yazeed Ce*
[12/3, 8:37 AM] ‪+234 803 308 6255‬: 💗💝💝💗
​*BUGUN ZUCIYA*​
   ( ​Heartbeat​)

                   💓💝💗
                        💗           

💓💝💗
​By​
     💗
    ​​*Fadeela Lamido*



           4⃣ to 6⃣




📓 Bakaramin firgita ma'u tayi ba lokacin da taga duna ya bude hannun shi ya cabe dutsen, cikin sauri ta sunkuyar da kanta dan gudun kar ya hangota"

    Shiru taji dan haka ta sake lekawa, baccinshi taga yaci gaba kamar ma bashi aka jefa ba, tintserewa ma'u tayi da dariya tare da fadin ashema magagi yake, katon banza baccin rana harda magagi, dariya ta kara sannan ta sake daukan wani ta jefa mishi"

     Wannan karon ahancin shi ya sauka amman ko motsawa beyi ba"

    Bakaramin dariya ma'u ke kwasa ba saida tayi me isarta sannan tace kash😬 ina ma na taho da waya dana mai photo nakaiwa su zee suga mutumin da sukejin tsoron sa ashema nauyin bacci gare sa harda su magagi"

     Wani dutsen ta sake dagawa, jin kiran sallah yasata zabura ta yarda dutse ta fito cikin takun kasaita ta wuce deeni tana kwambare kafada"

      Sai karfe 1:15 ma'u ta shiga gida, da fada mamata taryeta tana fadin"

     Asma'u wanne irin kunne gareki dazun2 nan abban Ki yace kidaina biyawa gidan dada amman dayake kunnen ki na kashi ne saida kikaje ko?


    Muryanta dauke da shagwaba tace, mama nifa bacan naje ba, tun dazun fah muna makaranta baba idi ne yasamu sharan masallaci"

    Fuskan mama dauke da rashin yadda tace sharan masallaci? Tsohowa bansan karya inace maza keyi?

    Tun yaushe aka daina basu, ai basu iyaba duk ranan da maxa sukayi baya sharuwa muko namu yayi kyau sosai malamai nata samana  albarkan Allah ya bamu miji nagari"

   
    'Da da mahaifi sai Allah, nan danan mama ta saki murmushi tana ameen  tsohowa Allah ya mike albarka"

    Cikin kunya tace amin sannan ta nufi dakinta"

     Kai tsaye toilet ta shige, wanka tayi sannan ta fito rike da kayan da ta cire tana kwalah kira goggo tani2

    Da saurinta ta shigo dakin tare da fadin Asmau lfy kuwa?

   Kayan ta mika mata tana fadin lfy lau goggo kayan mkrnt na zaki wanke min"

     Toh kuma gashi yanzun bani nake wanki ba, bala ne keyi amman bari nakai masa"

     Yar karamar riga ta saka tare da siket daidai guiwar ta, fitowa tayi tana tafe tana raira karatun al Qur'ani, afalo ta samu mama, cak ta tsaya lokacin da ta hango kayan makarantar ta agefen mama"

    Agogo ta daga kai ta kalla 2:10pm cikin fushi tace mama kinga goggo tani nabata kayan.....

    Dakatar da ita mama tayi da fadin nina hanata takaiwa bala kayan, goggon sa'arki ce ita dazaki dinga kwala mata kira kina danga daki, saikace sabowar mejego?

    Shiru tayi tana cigaba da zonburo baki"

   Mama taci gaba da cewa toh maza ki dauki kayanki kije ki wanke dan goggo tunda tayi ciwon hannu abban ki ya hanata wanki,  bala ne keyi, kuma ma bandan rashin hankali irin naki ya zaki hado harda bra dinki kice wai akwaiwa bala, yanzun ke bazaki iya wankewa ba acikin toilet"

    Mama nifa wlh abani duk wani aiki amman banda wanki" ni ban ma iya ba wlh"

    Toh aiko zaki koya maza ki kwashe kayan ki kije ki wanke babu me wanke miki agidan nan"

     Buga kafa ta fara akasa tare da kara kallon agogo cikin kuka tace"

   Mama nifah inason ne naje mkrntn yamma Kuma gashi yanzun lokaci ya kure, kuma idan banje yau ba duka na za'yi gobe"

   Karfe nawa kika shigo gidan nan?, ai suma malaman sunsan yau bazaku samu zuwa ba, tun da su suka saku aiki"

    Juyawa kawai tayi ta koma daki, dan bata da bakin mgn, kan gadonta ta fada, murmushi ta sake lokacin da ta tuna baccin duna, tare da wassafa fuskanshi a idon ta, mutun ne kyakyawa sai dai yaya akayi ya saka kanshi adaba, gashi duk anji mishi ciwo ajiki, da alama ma  bashi da karfi tunda yake bari na jimai ciwo, tsaki taja tare da fadin katon banza kana Yawo da wukake amman kana bacci atiti badole ayanyanke ka ba"

   Washegari tun karfe 7:30 ta nufi mkrnt bata biyawa zainab ba dan tasan bazata barta tai abinda tayi niyya yadda ya kamata ba"

     Tafe take cikin kayan mkrnt idan ka ganta gwanin ban sha'awa, ita ba dugowa ba ita ba gajera ba, fara ce tas, ga wani siririn hanci da bakin ta madaidai ci shekarunta basu wuce 16 zuwa 17 ba  amman kirjinta cike yake kai kace wata cikkakiya budurwa ce"

    Lokacin da ta isa kofar gidan da taga duna dubawa tayi ko ina babushi babu alamar sa, azuciyar ta taji babu dadi dan taso ace ta ganshi"

    Kad'a kai tayi ta wuce mkrt har aka tashi bata cikin natsuwar ta, Allah2 take atashi tabi hanya"

     Tana ganin akusan tashi ta tsiri rubutu, dan haka su rahama basu tsaya jiranta ba sukayi
tafiyan su"

    Saida ta dainajin hayaniyan yan mkrntr sannan ta dauki littafinta ta fito"

    Dakalin ta da ta ganshi akai jiya yauma yauma kwace yake agurin ya daura kafarsa daya kan daya, ya daura hula kan fuskar"

    Babu kowa alayin dan unguwa ce ta masu hali kowa yana cikin gidan sa babu ruwan wani da wani, hakan ne yaba ma'u daman isa gaban duna cikin sanda"

    Cikin siririyar muryanta ta rangada sallama taji shiru babu amsa dan haka ta gara matsawa daf dashi tare da tabbacin yauma baccin shi yayi nisa kaman jiya, ahankali ta daga hannuta ta dafa hular dake kanshi, jitayi be motsaba dan haka ta daga hular fuskan ta bai yana"

    Idon shi  rufe dan haka ma'u ta bude baki da hanci tana karemai kallo"

    Deeni wankan tarwada ne dan baza akirashi baki ba yana da duguwar fuska tare da dogon hanci daidai gwargwado, sakko da idonta tayi kan kirjishi da tat bai su kai kaca kaca dashi, yatsa ta cija sannan tace afili, meyasa kake bacci atiti bayan kuma ka sani sarai nauyin baccin gare ka, koni danake mace zan iya kashe ka ma ba jimaka ciwo ba, kallo ta kara masa sannan ta saka hannu ajakar makaranta ta dau waya ta daukeshi hoto har guda biyar sannan ta kwashe da dariya tare da fadin kai gskiya ni jaruma ce, agogo cikin wayar ta duba sannan ta nufi gida cikin sauri"

    Washegari ko ta nuna ma kawayen ta hotunan duna kaman yadda tayi niyya, mamaki ne ya kamasu tun daga ranan zee bata kara yadda ta jera da ma'u ba, dasu rahama take jerawa su jirata daga can gefe ta gama tsokanan duna tazo su tafi suna kyalkyalketa dariya"

    Ahankali wannan dabi'a tazama jiki agun ma'u kullum idan aka tashi mkrnt saita sameshi agurin yana bacci, haka zata gama surutun ta akan duna ta wuce gida"

    Haka har aka samu tsawon wata biyu ,wannan lokacin ma'u intaje gaban deeni bata sanda ko mgn ahankali dan tasan idan har yayi bacci idan kaso zaka iya daukan shi ka gudu"

    Abu ya zaman ma ma'u jiki harta kai alhamis da juma'a da babu makaran ta tana shiga damuwa dan haka yau juma'a da wuri ta isa dakin abban ta"

    Bayan ta gaida shi ta zauna daf dashi"

    Kallonta yayi da murmushi akan fuskanshi yace mamana ya akayi? duk yadda akayi akwai abin da kike so"

    Cikin shagwa ba tace abba na tuna Dada ne"

    Dada tana nan lfy mamana kulum tana cewa nagaishe mata da takwararta, ba inagaya miki ba?

     Eh abba amman ni inason ne naje naganta"

    Shiru yayi zuwa can ya dago yana share zufa yace, to naji amman kibari nasamu lokaci zan kaiki da kaina"

    Shiru tayi badan  ranta yaso ba, tana fitowa ta fara matso hawaye, karo sukaci da mama zata shiga dakin, ganin ma'u cikin hawaye yasa tabita da kallo"

   Alhaji yau kuma fada kukayi kaida maman taka?, naga ta fita tana share hawaye"

     Au kuka takeyi? Allah sarki, wlh ina matukar jin dadin yadda Asmau take nuna soyayyarta ga dada, amman kash bazan iya barinta ta zauna acan ba, sabo da gudun kar abinda ya faru shekarun baya yasa ke faruwa, shi yasa bana son na nuna mata gida biyu, kuma nacewa dada ta dawo ta zauna tare damu tace a,a bazan iya bari Asmau ta dinga zirga zirga atiti ba yau tana gida gobe tana gidan dada, dan gudun haduwa da gurba tattun samari"

    Mamace ta dago da kanta bayan ta gama sauraren shi ahankali tace alhaji Allah ne fah yake tsarewa, kuma ai be kamata ace anhanata zuwa gidan dada ba itama dadan ai bazataji dadi ba"

    Mikewa yayi fuskan shi babu annuri yana kokarin fita yace kice mata idan shirye take ta fito na sauke ta"

    Dagudu ma'u ta fito fuskanta cike da fara'a ta shiga motar ta zauna har suka isa bece mata komai ba"

    Akofar gidan ya sauketa sannan yace ki jirani idan nata so zanzo na dauke ki, ranta be soba, amsawa tayi ta shige gidan"

     Bakaramin dadi dada tajiba dataga ma'u, aikace2 gidan sukayi tare sannan suka zauna suna hira, suna cikin haka dada ta fara gyangyadi, ma'u naganin haka ta kalli agogo 11:15 tagani, zama tayi har taga 11:20 dan haka ta mike ta dauki bakin gyalenta agefen gadon dada sadaf2 ta fice"

     Da sauri take ta fiya dan taje ta dawo kafin dada ta tashi, tun daga nesa ta gane baya nan, dan gurin da yake kwanciya babu komai awajen, ja tayi ta tsaya domin taso ace ta ganshi"

     Gajiya tayi da tsayowa dan haka ta juya ta fara tafiya da nufin komawa gida, kaman ance ta juya ta hango shi kwace, kai yaya akayi haka? Ma'u ta tambayi zuciyarta, juyawa tayi cikin sauri ta isa gurin tare da sallama, jin babu amsa ya tabbatar mata da bacci ya wuce dashi daf dashi taje ta cire hular dake fuskanshi, idonshi rufe yake kamar kulum, fuskanta takai saitin tashi sannan ta huramai iska ahankali"

     Wani gwaron ajiyan zuciya ya Saki, da sauri ma,u taja baya"

    Ganin yaci gaba da baccin yasa ta sake matsawa ta bude baki ta sake hura mai fuska akaro na biyu, karaf taji anrike ahannunta"

     Subuhanallah yau nashiga uku na lalace, wayyo abba na waiyo dadata kuzo ku ceceni, dan Allah kayi hakuri

wlh takalmi nane ya tsinke na tsuguna zan dauka bansan akwai mutum agurin ba







Heartbeat
Mmn Yazeed🍁​
[12/3, 8:37 AM] ‪+234 803 308 6255‬: 💗💝💝💗
​*BUGUN ZUCIYA*​
   ( ​Heartbeat​)

                   💓💝💗
                        💗           

💓💝💗
​By​
     💗
    ​​*Fadeela Lamido*



              7⃣ to 9⃣




📚 Murmushi yayi kadan batare da yace komai ba, binta da wani mayan kallo kawai yake"

   Ma'u ko duk ta firgice tana rokon shi ya sakar mata hannu"

    Mikewa yayi tsaye batare da ya saki hannun ba, kuma har yanzun idonshi na kanta wani maya tatcen kallo yake mata"

     Cikin wata irin murya da bazata iya tattance yanayin sa ba yace"

    Ke baby natsu, bason gaddama, kishiga hankalin ki, kinji ko?

    Hannunta tasa duk 2 ta rufe bakinta tana daga kai alamar eh, acikin zuciyarta ko fadi take tawa ta kare"

     Menene sunan ki?

    Cikin rawar baki tace Asmau"

    Lumshe ido yayi sannan yasa ke cewa menene ya fito dake yau bayan babu mkrnt?

    Dan Allah dan darajan annabi kayi hakuri wlh daga gidan kakata nake, nasan yanzu tanacen tana nema na"

    Cikin wata irin murya yace baruwa na da wata kakarki ni ke kadai nasan.....

    Kukane ya kwace mata, cikin kukan tace to aini ban sanka ba wlh tsautsayi ne kawai ya kawoni nan, wlh da nasan haka ne da banzo ba"

    Murmushi ya sakeyi ahankali ya kara runtse hannuta cikin nashi, tare da lumshi ido"

    Zuwa can ya bude yace inace kinzo gadi nane?, dan kada abokan gaba su kawamin farmaki, dan kinsan nifa nauyin bacci gare ni, ke fah?

     😫 Nima inada shi wlh, narantse inada shi"

     Wannan karan saida yadan dara sannan ya dan jawota jikin shi tare da fadin baby ki kwantar da hankalin ki, bazan miki komai ba, jarumtar ki ta birgeni, ni jarumi ne dan haka inason naga mace jaruma, kin yi kokari sosai dakika tunkare ni, amman meya hana kika kasa hakuri zuwa gobe asabar kika fito yau?

    Ainace maka gidan kakata naje yanzun ma tsautsayi ne ya fito dani"

     Hmmm kawai yace sannan yaja hannuta zuwa gurin kwanciyar shi ya zaunar da ida"

   
     **

  Aban garen dada kuwa da misalin 12:09 sallama alhaji  ne ya tasheta daga bacci"

     Afirgece ta tashi tana fadin takwara shine baki tasheni baccin ba bayan kinsa ina tafiya masallacin juma,a da wuri"

     Gaba dayan su wurga ido suke suga ta ina ma'u zata bullo daga abba har dada"

     Jin shiru yasa dada ta shiga kwala mata kira taji shiru, mikewa tayi azabure tana fadin zoka zauna inaga ta shiga gidan tabawa bari nakirata"

     Zama yayi kamar yadda dada tace sannan ya cire hular kansa ya aje agefe, tare da fadin Hmmm Allah ya kyauta"

    Lokacin da dada ta shiga gidan ta bawa cemata tayi ko kallita bata gani ba, dan haka tayo waje hartana tuntube"

     Azauren suka hadu da dan tabawa yana kokarin shiga gidan, kallon shi dada tayi tace kai iro baka gamin Asmau ba?

    Aiko dazun naganta nan wajen hanyar mkrtnr su......

   Bata bari ya rufe baki ba tabi hanya tana gudu2 sauri2"

    Kalu innalillahi wa Inna ilaihir raju'un ta fada lokacin da ta hango ma'u rike hannun Duna"

    Jikintane ya fara rawa bata San sanda ta kwasa aguje ta nufi gida ba"

    Ganin dada agoje abin yabawa iro daya biyo bayan mamaki, shan gabanta yayi dan gudun karta tuntsura, riketa yayi tare da fadin dada lfy menene ya faru?

    Ajiyan zuciya ta fara bata iya cewa komai ba saijan hannun iro take"

      Daga nesa tamai nuni dasu, lokacin suna zaune ita da Duna"

    Salati yayi sannan yace dada, ki tsaya inwuce saiki kwala mata kira tunda ke tsohowa ce kila bazai miki komai ba, amman ni idan ya ganni akwai matsala dada, tunda shi fadan shi baya wucewa inda kikasan shedan haka yake, cikin sauri iro yabar wajan yana me Kara karfafawa dada guiwa da hannun shi"

     Tashin hankali ne sosai azuciyar Dada, kafafuwanta banda rawa babu abinda suke, kallo ma'u tayi tana mamakin yaya akayi ma'u tasan deeni harta bari suka zauna guri daya , kuma da alama ba tursasata yayi ba, kawar da tunanin tayi sannan ta daga murya ta kwalawa ma'u Kira"

    Tana hango dada ta mike azabure, ta nufota aguje, ganin haka duna ya mike ya biyo bayanta"

   Takaici ne ya kama dada dan haka ma'u na isowa ta daga hannu ta sharara mata mari, hannu ta sake dagawa zata kara mata, taji andaka mata tsawa cikin wata irin murya ta kyauraye"

   Ke ! Ke!! Yasin yasin kika sake hannunki ya kara kaiwa jikinta sena sassara ki, Allah wlh *gunduwa gunduwa* zanyi dake, yasin hannunki ya kara kaiwa jikin ta kigani"

   Suman tsaye dada tayi, fita tayi daga hayyacin ta, lokacin da network dinta ya dawo gani tayi suna tafe ita da ma,u sai janta take, tana kara fadin dada taho mana"

   Bata iyace mata komai ba illah binta da take da kallo, sai dai akwai tashin hankali karara a idon ma,u"

   Sauri ta kara dan sai yanzun ta tuna abban Asma'u yana gida yanajiran su, jitayi kaman lema ajikinta dan haka takai idonta kan zaninta jike yake sharkaf nan ta tabbatar fitsari ne"

    Suna karya kwanan layin, ma'u ta hango abbanta sai zagaye yake akofar gidan dada, gefen shi iro ne azaune ya rafka uban tagumi"

    Hunnun dada ta matse tare da fadin wayyo Allah na, nashiga uku"

    Kallota kawai dada tayi ta tabe baki tare da fadin Hmmm"

   Jikin ma'u ban da rawa ba abinda yake, cikin mtsanan cin tashin hankali ta taja ta tsaya tana me tsiyayar da hawaye dan ta tabbatar yau kashinta ya gama bushewa"

     Ganin abba na tahowa yasa ta faraja da baya ahankali, tana kokarin rike Dada"

    Yana isowa yasa hannun shi ya rabata da jikin dada ya zaf ga mata mari har saida ta fadi kasa, cikin karaji yace daga gidan uban wa kike?, jin da yayi babu amsa yasa ya daga kafa ya nufi cikinta yana kokarin tokarin ta aciki, tare da fadin badake nake mgn ba?

    Cikin matsanan cin firgici dada ta rike Abba da wani irin karfi da batasan tana dashi ba, tana fadin kasheta zakayi ne?, toh bismillah nunamin yarka ce, nace kanuna min ka haifa kuma ni mahaifiyar ka ban isa na aiki yar ka ba"

    Sanyi jikin Abba yayi, cikin natsuwa ya shiga bata hakuri, badan ya yarda cewa dadan ce ta aiketa ba"

    Haka dada taita fada abba nabata, hakuri da karshe da kanta tasa ma,u amota abban ta, tana cigaba da fada"


    Dada na tsaye akofar gida har motan abba ta bace, ajiyan zuciya ta sauke sannan ta juya ta shiga gida tana mamakin inda ma,u tasan deeni"

    Kulle gidan tayi da sakata domin ita har yanzun gani take kamar duna zai shigo mata gida dan ba karamin tsorata tayi ba, wanka tayi ta gyara jikinta sannan ta wanke kayan da ta cire ta shanya, aranan dada bata runtsaba data rufe ido duna take gane"

      Asmau kuwa suna isa gida ta sauka aguje tayi cikin gida"

     Binta da kallo Abba yayi tsananta me tsanani yaji acikin ransa dan haka bayan ya shiga falon ya zauna, ma'u daga daki taji yana waya yana fadi"

    *Usman* na gari ne?, toro mun shi yanzu yanzun nan, akwai matsala"

     Faduwa ma'u tayi daga kan gadon dan ta tabbatar yau sai dai buzun ta indai ta bari har ya usman ya riketa"

 
       *WAIWAYE*


    Alhaji sani haifaffen jahar Kano ne, su 2 iyayen su suka haifa, daga shi sai yayan shi Alhaji musa, alhaji sani shine mahaifin Asmau, su uku suka haifa, tare da matar sa Fatima, usman shine babban, sannan fiddausi sai yar auta asmau wacce taci sunan kakanta"

    Shiko alhaji musa Saida ya shikara 15 be samu haihuwa ba, dan haka kaninsa alhaji sani ya bashi danshi usman alokacin yana da shekara 5"

    Usman ya taso cikin gata gidan alhaji musa tamkar dan da suka haifa da cikin su, yayin da alhaji sani yaci gaba da kula da fiddausi wadda take yar shekara 2"

     Alharji sani da yayan sa ma,aikatan gwamnati ne, kuma suna samu daidai gwargwado dan a unguwar su idan xa ai lissafin masu hali baxa a kirga 5 babu su aciki ba"

     Fiddausi nada shekara 10 aka haifin Asmau, tun daga kan asmau basu sake samun haihuwa ba"

     Bayan shekara 8 fiddausi ta zama cikakkiyar budurwa meji da kanta duk abin da take so shi ake mata, saidai abu daya abban su baya barin yawo indai ba gidan dada tace zataba ba a barinta zuwa ko ina, dan haka lokacin da ta kare secondary ta samu daman tafiya jami'a ta balle bishashanta acan, ahankali fiddausi ta zama bata da abokai sai maza, haka zaka ganta tsakiyar maza ita kadai mace"

    Babu wadda keda lbrn halin da fiddausi take ciki amakaranta, dan da antashi gida take yowa dan tasan ko minti 10 takara sai ance inata tsaya"

    Ana haka maza suka fara canzawa fiddausi tunani domin ko duk abokanta kusan su 7 babu wadda baya lalubeta da sunan wasa, dan haka ta farajin babu abin da take so illah taga ta kadai ce da namiji"

    Duk abinda suke sauran dalubai na kula dasu, yayin da wasu daga cikin matan suke tur da halin fiddausi, ita kenan yau ka ganta manne jikin wancen gobe jikin waccen"

    Yauma kamar kullum tana cikin motar wani abokinta KB suna manne da juna ita da kanta ta lalubo bakin shi ta cusa nata ta, saida suka gama shagala, sanna ta gabatar mai da kudurinta"

    Murmushi KB yayi dan yasan za'ai haka, yayi mamaki ma da har aka kawo yanzun bata bada kai ba, sabo da salon da suke mata"


     Kwantar dakai KB yayi tare da fadin babu damuwa, amman fa saidai kizo muje Ki tayani kwana"

    Zaro ido tayi dan tasan zancen shi bamai yuwuwa bane, tace KB ? Kana son Abbana ya kasheni ne?

    Tsaki yaja sannan yace haba meyasa kike abu kamar wadda bata waye ba, ai dibara zaki masa"

     Bayan kwana 2 fiddausi ta kasa hakuri dan haka ta shirya tayi sallama akan zata gidan dada ta kwana"

       Gidansu KB ta wuce wadda har ya kaita da kwana adakin kb kuma har komai ya kasan ce, karfe 7:09am ta isa gidan dada da kayanta ajaka kamar yadda ta shiryu, ganin inda take tattale kafa yasa dada fadin ke lfy meya sameki kike wani tafiya saikace agwagwa"

     Akafa fah na taho dada wlh gajiya nayi"

    Ruwan wankan dada ta juye tayi wanka tare da gasa jikinta, ko karyawa bata tsaya yi ba, ta  haye  gado sai bacci domin KB be bari ta runtsa ba"

     Damisalin karfe 8 alhaji sani ya iso gidan ganin fiddausi agado hankalin shi ya kwanta"

    Tun daga ranan wannan dabi'a ta zaman mata jiki har saida ya kasance gaba dayan su 7 sun gama sanin wacece fiddausi"

     Ankwashi tsayon watanni ana haka kullum fiddausi tana hanya wata rana takan kwana gidan dada amman sauda yawa dakin samarinta take wucewa idan ko har ta kwana gidan dada toh safiya nayi zata wuce gurin samarinta, babu wadda ya lura da halin da fiddausi take ciki har saida fiddausi ta fara rashin lfy, ana zuwa asibiti gwajin farko aka shaida musu tana dauke da ciki Wata 2"

    Mummunan tashin hankali suka shiga ba kadan ba, wadda da takai har abba ya kwanta asibiti saka mukon hawan jini daya kamashi,

    Duk abinda ake usman bashi da lbr dan lokacin yana mkrnt yana kokarin karasa karatun shi na soja"

     Bayan abba ya samu sauki ne suka zauna da yayan shi alhaji musa tare da sanya fiddausi agaba ta fada musu wadda ya mata ciki"

    Tashin hankali ba'a sa maka rana nan idon fiddausi ya raina fata damin kuwa acikin abokanta guda 7 babu wadda baya kusanta ta dan haka batasan sunan Wa zata kira ba








    Heartbeat
Mmn Yazeed🍁​
[12/3, 8:37 AM] ‪+234 803 308 6255‬: 💗💝💝💗
​*BUGUN ZUCIYA*​
   ( ​Heartbeat​)

                   💓💝💗
                        💗           

💓💝💗
​By​
     💗
    ​​*Fadeela Lamido*



          🔟 to 1⃣1⃣




📓 Nadama ce me tsanani ta shigeta cikin kuka ta furta KB, koda alhaji musa yasa aka binciko masa KB nunawa  yayi ai bashi kadai ke nemanta ba dan ko satin daya wuce a dakin abokin sa ballo ta kwana, dan haka babu wadda ya isa yace ciki nasa ne"

    *Bugawa* zuciyar abba tayi jin yarshi tana kwana dakin maza, duk irin tsaron da yake bata, hawaye masu dumi suka fara zubo masa"


    Ganin inda abba ke zubar da hawaye hankalin fiddausi yayi mummunan tashi, acin  kuka tace abba dan Allah kayi hakuri ka yafemin"

    Mikewa KB yayi yana fadin ni kar a kara kirana akan wannan xancen danni tun farko ita ta nemeni gatanan ku tambayeta cewa tayi intaima keta"

     Fashewa abba yayi  da kuka kaman karamin yaro, alhaji musa ne yace bazaibar xancen ba, yan sanda yasa suka kama KB, cikin bin ciken su suka kama mutun 7 da fiddausi take kwana dakin  su"

    Lokacin da abba yaga tika2 maxan da fiddausi ke kwana agurin su abin ya bashi tsoro kuma gashi kamar hadin baki dan kowanne cikin su cewa yake ita tace ya taimaketa"

     Nan take abba ya fara aman jini, asibiti aka nufa dashi kai tsaye, satin shi 2 asibiti ya fara samun sauki"

      Aban garen fidausi kuwa tunda tasamu lbr rashi lfyn abba kulum cikin kuka take, figewa tayi ta lalace gawani uban baki da tayi"

     Kwata2 mama bata mata mgn , ko gaidata ma da takeyi cewa tayi idan ta Kara mata mgn Allah ya isa"

    Rayuwa tayiwa fiddausi zafi haka zataita kwara amai mama naji amman ko kallota batayi adaki take zama tace kukunta takoshi, hakika fiddausi tasan ita ta basu KB dama amman ai su sukasa hartakai wannan matakin saboda irin wassannin da suke mata, kuka taci sosai tundaga ranan ta kama rashin lfy"

    Satin ta daya adaki bata ko iya tashi, goggo tani ce tashiga dakin dan taji shirun fiddausi yayi yawa, samunta tayi duk ta rame ta tsutse gashinta baje akan gado bakinta ya bushi yayi wani bawo2"

     Furgita sosai goggo tayi tana xare ido tace ke kina cin abinci kuwa?

    Ruwa ruwa kawai fiddausi take fadi"

     Tashin hankali sosai abba ya shiga lokacin da dada takai mai lbr"
Hakika yana matukar son firdausi saidai wannan Abu data aikata yana sosa masa zuciya"


    Firdausi naganin abba ta fara rokonshi da girman Allah ya yafe mata tari ne ya kwace mata, babu kyaukyautawa dan haka hankalin kowa ya koma kanta"

     Zuwa can jini ne ya fara fita ta baki ta hanci, cikin rudu abba ya wuce ya tallabeta tare da fadin firdausi na yafe miki, kuma zanci gaba da addu'a duk wadda ya lalata miki rayuwa uban giji Allah ya saka mike"

    Murmushi tayi kadan sannan ta jawo hannun mama ta rike acikin nata, ta karyan da kai alaman roko"

     Mama ta fahimce ta, itama karya kai tayi hawaye na sauka afuskanta tace na yafe miki duniya da lahira"

    Murmushi tayi sannan ta daga hannu tanawa su dada bye bye✋🏻"

     Abba ne yace ya kamata mutafi asibiti dan naga jikin ya matsa mata"

      Murmushi firdausi tayi tare da girgiza kai tana mutsa baki"

     Ahaka abba da alhaji musa suka dauketa suka nufi asibiti, banda murmushi babu abin da take"


      Emergency aka shiga da ita, yayin dasu abba sukai cirko2, zuwa can likintan ya fito yana share zufa tare da fadin alhaji saidai kui hakuri dan *zuciyar* yariyar yariga ya *buga*"

      Mekake nufi? abba ya tambaya yana me kallon cikin idon likitan"

      Cikin sanyin jiki yace ta rasu"

     Innalillahi wa inna ilaihir raju,un shine abin da kuwa yake cewa agurin"

  Lokacin da abba ya tsaya akan gawan Fardausi,  Hawaye ne sosai yake fita a idon shi kanta ya dafa yace Allah yajikan ki Allah yasa mutuwa ta xame muki hutu, kukane yaci karfin sa dan haka alhaji Musa ya kamashi yayi waje dashi"


     Bayan ankwai Firdausi gidanta nagaskiya ne alhaji musa ya tura adauko usman"

     Bayan isowan usman ya shiga munmunan tashin hankali, kuma yaci alwashin daukan fansa agun su KB"

     Abba cewa yayi babu wani fansa daza,a dauka duniya ce wadda bezoba ma jiransa take dan haka abar ma Allah"

      usman ya koma makaranta bayan sadakar 7 mama da Abba kuwa sunfi shekara 1 suna cikin jimamin Abba yau ciwo gobe lfy"

    Wannan dalilin yasa abba ke matukar sawa ma,u ido tare dayin kaffa2 da ita"

    Ayanxun usman ya gama karatun shi ya zama cikken soja kuma yayi aure shekara 1 data wuce

      itako ma'u awannan watan ta kare secondary dan haka yanzun islamiya kawai take zuwa"



 *CIGABAN LABARI*


Dakin baccin mama ta nufa aguje tana fadin mama dan Allah karki bari yaya usman ya dakeni wlh dada ce ta aikeni.....

    Fita kiban guri cewa mama dake nunawa ma'u hanya"

    Kuka ta fara tana rokon mama tsayowar mota taji dan haka ta ruga dakinta"

      Usman ne ya shigo falon tare da matarsa Fa'iza, bayan ta gaida abba ta fita ta basu guri"

      Abba ne ya kwashe duk abin da ya sani ya fada ma usman, shiru yayi zuwa can ya mike yace abba bari naganta"

   Kofar dakin ya tura ya shiga, ma'u na tsugune agefen gado idon nan zuro2"

    Zama yayi agefen gado sannan yace ke zonan"

     Bata iya mikewa ba da rarrafe ta matso, jikinta sai kerma yake"

     Ina kikaje?


     Toshe bakinta tayi da hannunta hawaye na zobowa afuskanta tace"

     Yaya narantse dada ce ta aikeni, kuma ka tambayeta ka......

    Wani uban tsawa usaman ya buga mata wadda yai matukar razanata, sannan yace"

    Wasa nake dake?, zaki gayamin inda kikaje kosaina karya ki tukuna?

    Mikewa tayi arude tana fadin yaya dan Allah karka karyani wlh dada ce ta aikeni "

    Mikewa taga usman yayi yana nan nade hannun rigar sa, uhu ta bara lokacin da taga yana kokarin kwance ma dauri wandon sa"

    Batai aune ba ta farajin saukan duka, yana dukanta ne yana gara tambayanta inda taje amman har yamzun mgn daya take maimai tawa dada ce ta aiketa, dan haka usman be dena dukanta ba har saida yaga ta kasa tashi, ihunta ma ya daina fita sannan ya tsagaita"

    Bakin gadon ya koma ya zauna sannan yace kince dada ce ta aike ki dan haka inason ki gayamin inda ta aike ki"

     Tsintan kanta tayi tana fadin carbin ta ne ya tsinke tace nakai mata gyara"

         Carbi? Jitayi yasake hada mata mari akumatunta duka guda biyu, bata kara sanin inda take ba"

      Zuwa can ta bude ido taga matar yaya usman zaune agefenta tana mata fifita"

     Muryanta adashe tace anty Fa'iza kina gidan nan kikabar yaya yana neman kashe ni?

    Rufe mata baki tayi idonta cike da kwallah  tare da fadin Asmau naso na shigo mama ce ta hanani"

    Kuka ma,u taitayi Anty Fa'iza na lallashinta"

    Washegari da safe ma,u ta tashi jikinta ya mata tsami ga fuskanta duk ya kunbura, jin muryan dada afalo yasata farin ciki , tashi tayi tana takawa ahankali ta fito falo"

    Salati dada tasa lokacin da idonta ya sauka afuskan asmau sannan ta juya ta kalli abba tace"

    Au yanzun nan saida ka duki yariyar nan?, aida kasani ka hada haddani tunda nice babban me laifi, amma ba komai Allah ya baka hakuri, juyawa tayi zata fita ranta bace"

     Hakuri abba yaita bawa dada, daker ta yadda ta dawo, rike asmau tayi suka shige daki, bayan sun zauna ne dada ta kalli asmau cikin tohuma tace"

     Toh asmau mgn nazo muyi me mahimmanci, kuma inason kisa aranki wannan mgn tsakanin ni dake ne babu mejinta"

    Gyada kai ma,u tayi tana share ragowan hawayen dake fuskanta"

     Asmau menene tsakanin ki da wannan ibbilishin yaro?

    Shiru tayi tana kallon kafar ta, tare da zubo da wasu sabbin hawaye"

     Takwara badake nake mgn ba?

    Cikin kuka tace dada ni wlh babu komai tsakanina dashi ahankali takwashe duk yadda akayi ta gaya mata"

    Shiru dada tayi tana mamakin hali irin na asmau, ace yariya ba'abin da tasa agaba sai tsokana, zuwacan ta kalli ma,u sannan tace"

    Karki kara irin wannan rashin hankalin, ban da kuruciya me ya dameki dashi? Mutumin da manya ma gudunshi suke, shine ke zakina shige mishi?, kinatsu sosai kisan me kike keba karamar yariya bace, koko so kike kisa ubanki atashin hankali?

   Girgiza kai tayi sannan tace aina bari bazan sake kulashi ba kuma dan Allah idan yaya usman ya tambaye kice kika aikeni"

    Hmmm takwara kenan, naji kuma zan fada amman saikin min alkawarin baxaki sake kula wannan shaidanin yaron ba"

    Har cikin zuciyarta batajin dadin sunan da Dada take kiran deeni, dan haka saida ta runtse ido sannan tace, nayi alkawari"

      Bayan kwana biyu jikin ma,u yayi sauki saidai har yanzun akwai shaidan duka ajikinta kuma fuskanta be gama sabewa ba"

     Shiryawa tayi cikin kayan mkrnt sannan tayiwa mama sallama ta wuce"

     Wata zuciyar ce tace kibi ta gurin mana ko hangoshi ne kyayi daga nesa,  a'a nayiwa dada alkawari ta fada afili, koda takai daidai lungun fasa bi tayi dan jitake idan bata gansa ba kaman wani abu zai faru"

    Tunkafin ta isa gurin ta hangoshi sai waige2 yake kamar dai yana neman wani, zuwa can ya juyo da kallon sa, gurinta, wani munafukin murmushi ya sake sannan ya fara tahowa"

    Kaucewa ma,u take, tare da kara sauri, amman duna sai dad'a binta yake"

      Ganin haka ma,u tasa kuka, tare da tsayawa cak"

    Wani irin kallo yake mata, tare dason kallon kwayar idonta, zuwa can ya mika hannun sa ya shafi kuma tunta shedan yatsu ya gani kwance"

    Nan danan idonshi ya rikice ya kuma jawur, sannan ya karkata kai yace"

     Shedan hannun waye afuskan ki?? uban waye ya dake ki??

   Jikin asma'u banda kerma ba abin da yake, agigice ta kauce tana kokarin guduwa"

    Damkanta yayi tare da fadin ina wasa dake ne? Ashe yau unguwar nan babu zaman lfy indai baki fadamin wadda ya bata miki fuska ba ton wlh duk wadda nagani sara ne"

    Rudewa asma'u tayi cikin kuka tace a'a wlh yaya nane"

    Yayan ki?, toh wlh sainaci uwassa, zai shaida cewa bakin rijiya bawajen wasan makaho bane, yasin saina canza mai halitta


   
Hannu ya zura aljihu ya dauko wata karamar waya ya danna sannan ya kara akunnen shi, zuwa can taji yana fadin *Shazali* ka hadu min  karnukan nan ka kawo su yanzun nan, kacewa *Caka* ya  tahomin da *Duna* yau akwai aiki idan ba ayi wasa ba saina mai yankan rago



      Heart Bear
   *Mmn Yaxeed*🍁​
[12/3, 8:37 AM] ‪+234 803 308 6255‬: 💗💝💝💗
​*BUGUN ZUCIYA*​
   ( ​Heartbeat​)

                   💓💝💗
                        💗           

💓💝💗
​By​
     💗
    ​​*Fadeela Lamido*




*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*



         *Na sadaukar da wannan shafin gareki👇*
        👑Queen👑😘

 *Nima ILove u wojuga wojuga wlh😍*🍭



      1⃣5⃣ to 1⃣6⃣




📒 Jin ya ambaci gaisuwa ce yasata jan jikinta ta koma gefe, tare da karabin karan da kallo"

    Haryanzun hijjabinta na bakin shi, matsowa yayi ya ajiye hijjabin akasa sannan ya koma kusa da deeni yana goga kanshi ajikin deeni"

     Sai alokacin ma'u ta tuna jikinta babu hijjabi hannu tasa ta rufe kirjinta, sannan ta matsa ta dauki hijabinta ta saka"

     Karan tabi da kallo har yanzun Yana gaban deeni sai shafamai kai yake alman lallashi"

    Tsaki taja azuciyarta sannan tace wannan bakin karan ne duna, ganin inda yake lallashin karan abin yai matukar bata haushi, hawaye ta fara matsowa acikin zuciyarta tace  yanzun akwai miyon wannan mumman karan ahijjabi na wlh Allah ya isa, bata san cewa mgnr ta fito fili ba saiji tayi deen na fadin wa kikeyiwa Allah ya isa.....

    Atsora ce tace ni bada kai nake ba, da wannan mummunan karan naka nake"

    Ke *duna* kike kiran mummuna kinyi na farko yariya karki kara, idan kuma kika kara zan barki dashi"

     Kallo kawai ta bishi dashi har yanxun lailaya kan Karen yake, harga Allah haushi yake bata dan me xaisa hannun sa yaita shafa kare batasan lokacin da tace toh kadaina shafashi haka mana"

     Inaruwan ki ko kanki nake shafawa?

    Kasa tayi dakai tana cigaba da kunkun"

    Tunda ta fara motsa bakinta deen
yake kallon bakin amman ya kasa gane kalma daya da take Dada dan haka yace banajin abinda kikecewa"

    Turo baki tayi sannan tace  ai badakai neke ba"

  OK da *Duna* kike kenan?

     Shiru tayi batare da tace komai ba dan haka deen yayiwa caka mgn da hannusa gani tayi ya matsa can gefe ya tsaya atsakiyan hanya"

    Kallonta ta mayar kan deeni gani tayi ya dago kan *Duna* yana mai mgn da ido aguje yayo kanta tare da haushi irin na mahaukatan karnuka"

    Cikin gidan su deen tashiga aguje ummi na zaune tana wanke2 tayi fatali da ruwan cikin jikita ta shige ta kwakumeta"

    Kobata tambaya ba tasan karen deen ne ya biyota dan tun dazun takejin haukan sa, rungumeta tayi ajikinta tare da fadin uban gidan nasa baya wajen ne ya bari yana tsorata Ki?

    Sai alokacin kuka ya kwace mata cikin kukan tace ai shine yace mai ya biyoni"

    Daidai lokacin deen ya shigo yana murmushi harara ummi a zubamai sannan tace nadai hanaka shigowa da karan nan uguwar nan kaki bari ko?

     Ummi nakawoshi ne yagaida wannan yariyan ita kuma sai zaginshi take"

    Ai dole ta xageshi auta tunda bata saba ba ita gani take tsoratata yake,  yanxun zoka rakata ta shiga makaranta"

    Makaranta ? Yau bazata makaranta ba lokacima ya kure"

    Bude baki ummi tayi xatayi mgn amman deen sai ya mata wani irin siririn fito tare da kada mata hannu nan danan taja bakinta ta tsuke , shiko deen dakin sa ya shiga"

     Daga ma,u har ummi tsaye suke saidai jikin ummi asanyaye yake kamar tana cikin damuwa"

     Zuwa can ta waigo tace Asmau dan Allah ga abincin auta nan a kitchen taimaka ki kai masa rabon sa da abinci ya dade basan me yake damunsa ba"

    Shiru ma,u tayi kanta akasa acikin zuciyarta tace toh meyasa bayacin abinci? Afili ko cewa tayi ummi wlh tsoron shi nakeji"

    Murmushi ummi tayi sannan tace a'a karkicemin kinajin tsoron sa keda mutumin ki kuma? bubu abinda zaiyi miki tashi maza kije"

    Jikinta babu kwari ta nufi dakin da taga deeni ya shiga sallama tayi abakin kofar bayan ya amsa tashiga"

     Dakine dan karami daga can gefe akwai yar karamar katifa gefen katifan ko wukakene an jigine su a jikin bango"

    Gyare dakin yake tsaf ahankali ta karasa gaban katifan ta aje kwanan tana kokarin mikewa ya rike hannun cikin sauri ta dago ta kalleshi"

    Ido suka tsurawa juna natsayon wanni lokaci take ma,u taji tsigan jikinta na tashi nan danan idonta yacika da kwalla amman takasa dauke idonta akanshi"

    Shiko deen wani irin farin ciki yakeji wadda betabajin irinsa ba har yanajin inama su kwana ahaka"

    Murmushi yasaki wadda yai matukar dacewa da fuskanshi azuciyar ma,u cewa tayi inama ace haka fiskarshi take kullum"

    Kasa ta sauke idonta tare da sauke ajiyan zuciya, haka shima deeni ajiyan zuciya ya sauki sannan yasa hannun shi ya sake dago fuskanta"

    Runtse idonta tayi cikin wata dashashshiyar murya taji yace *Asmau* bude idonki ki kalleni"

    Koro na farko da deeni ya kira sunanta agabanta dan haka taji yafi kowa iya kiran sunanta"

    Bude idon tayi saidai baxata iya kallon sa ba kamar yadda yace dan haka ta durkusan da kanta kasa"

    Jawota yayi daf dashi ya zaunar sannan yace meyasa kwana 2 baki zuwa makaranta?

    Ina xuwa ta fada atakaice"

    A'a karya ne bayan kullum inajiran ki akofar gida amman ban ganin wucewan ki"

   Wlh kullum ina zuwa bandai wucewa ta nan ne "

     Me yasa ?

  Shiru tayi tana tunanin tagayamai abbanta yace zaiyi mata aure ne ko karta gayamai, idan bata gayamai ba toh mezata cemai?

    Tunanin me kikeyi?

    Bakomai "

  Shiru yayi xuwa can yasake dagowa yace yau kinji ganina kenan shine kikazo kina leka mana gida"

     Turo baki tayi kaman zatai kuka zuwa can taji ya sake cewa  wadda ya dauki ki a mota ranan shine babanki?

      Eh tace tare da kurawa kirjin shi ido"

    Shiru yayi yana kallonta zuwa can yace me kike kallo?

    Kai tsaye ta nunamai sarkan dake wuyan sa"

   Kina sone?

  Tana wasa da yatsunta take fadin a'a kacire ne beyi maka kyauba"

    Dariya yayi sosai har hakoran shi suka baiyana zuwa can yace naji tunda bakison ganina da sarka saikizo kicire da kanki"

     Tana cigaba da wasa da hannunta tace kacire da kan ka ai babu kyau mace ta dinga taba namiji"

    Axuciyar shi yace kina da wayo babu kaifi afili kuwa cewa yayi toh bakison nadaina sawa kenan?

    Mikewa tayi tare da fadin nixan tafi kar atashi amakarata bansani ba"

    Daure fuska yayi sannan yace dawo ki zauna, idan lokaci yayi zan fada miki"

    Zama tayi nesa dashi badan ranta yaso ba, kanshi ya turo mata ahankali ta fara warware sarkan duguwa ce sosai, kallon sarkan take tana mamakin wai mutum da hankalin sa ya dauki wannan karfen yasa ajikin sa"

    Shiko deeni kallonta yake yana murmushi yana da tabbacin yadda *ZUCIYAR* shi ke buguwa haka ta ma'u ma take bugawa, xuben da ke karamin yatsan shi yacire ya kamo hannun ma'u ya zura mata"

     Harcikin zuciyarta taji dadi kallon zuben tayi sannan tace nagode"

    Murmushi yayi sannan yace toni me xaki bani?

     Tsintan kanta tayi da cewa me kakeso na baka?

     Duk abinda kika bani zanyi farin ciki dashi"

     Cikin sauri ta ciro xoben da abban ta ya saya mata ta mikamai"

    Nuke kafada yayi kaman yadda yara keyi yace bazan karba ba, ni ai saka miki nayi dan me xaki bani ahannu"

     Shiru tayi cikin rashin jin dadi zuwa can tace ka karba ai be dace bane ina mace kuma.. ..

     Kasa karasawa taayi dan haka deen yaja tsaki ya kwatar da kanshi akan katifan"

   Ganin haka yasa ma'u taji babu dadi dan haka ta kamo hannun saidai duk yatsan da ta nufa zuben baya shi, daker ya shiga karamin yatsan shi, shima be gama shewa ba"

     Tagama sawa tana kokarin mikewa ya mirginota jikinsa ya rungumeta tsam ajikin shi, tare da sunbata goshinta kumatunta zuwa kan lebenta, neman rikicewa yake, dan haka ma'u tafara kokari kwace kanta take mgnr abbanta ya fado mata,  hawaye taji yana zubu mata"

    Daidai lokacin ummi ta dago labulen cikin sauri deen ya mirgina ma'u gefe sannan ya cigaba da sauke ajiyan *ZUCIYA*"

     Cikin sauri ma'u tamike tana gyara hijjabinta"

    Itako ummi kallon deen take cikin bacirai zuwa can tace auta har ka manta alkawarin dakamin?

      Be iya cewa komai ba dan koya bude baki besan me zaice ba"

      Yana kwance yanajiyo fadan ummi, dakanta ta rike ma'u tayo waje da ita"

      Jin asmau zata tafi yasashi mikewa dasauri ya fito samu yayi daidai ummi ta budewa ma'u kafar cikin sauri ya rike hannuta tare da zuba mata jajayen idon shi sannan yace gobe zaki zo ?

      Tana share hawaye tace eh"

     Murmushi yayi kadan sannan ya karkata kai"

         *****

Tafe take tana kuka dan daganin yanayin garin andade da tashi makaranta"

    Ta saka wannan ta kwance wancen tana tunanin wata karyan zata shirya"

    Taci rabin ta fiya taga motar yaya usman ta wuceta"

    Innalillahi ta fada azuciyarta Allah yasa be ganeni ba"

     Hango motar tayi ta tsaya tana dawowa da baya"

    Jitayi 'ya'yan hanjinta na motsawa daidai saitinta yaya usman ya tsaya ya zubo mata idonta shi sannan yace ke sai yanzun kike dawowa daga makarantar?

     Mutumin dake zaune agefen shi ta kure da ido, gani take kaman kunki ne domin kwata2 baya motsi, jarida ce bude ahannun shi  idonshi sanye da farin glass"

    Yaya usman ne yace kagamin shegiyar yariya ina mata mgn tana kallon wani guri"

     Zabura tayi ta dawo cikin hankalinta ta kara matso kuka tace"

    Yaya wlh kare ne ya tareni ahanya ya hanani wucewa.....

   Kutumar ubanki shigiya yar iska, ni xaki rainawa hankali duk cikin daluban be tare kowa ba saiki ? A ina kika tsaya?

    Cikin kuka ta tattaro hijjabinta tace wlh yaya da gsk ne kagama yadda karan ya lalatamin hijjabi"

   Takaici ne ya kama usman dan haka yace Allah ya kara, dayasani ma ya ciccije ki dan ubanki, kin tsaya shashanci duk dalubai sun wuce sun barki dallah dobeki saikace doluwa, ni shiga mota mutafi"

    Tashiga mota? mutumin dake kusa da yaya usman ya tambaya  batare da ya waigo ya kalleta ba har yanzun idonshi nakan jaridan"

    Waigawa usman yayi ya kalleshi sannan yace wannan itace kanwata *Asma'u* danake baka lbr, wlh kwata2 yariyar nan batajin mgn"

    Idonshi akan jaridan yace aina ganeta, kanta na rawa, naji kaman kana cewa ta hau mota, ai kamata yayi ta isa gida kafin mu isa"

    Kumafa hakane usman ya fada yana kallon ma,u zuwa can yace  asmau kafin mu isa gida nasameki acan, idan har kika bari na rigaki isa gida kashinki ya bushe"

    Arude tace yaya amota kake fa ?

   Muryan bakon taji yace ke!!, dakaran ya yabiyoki bakiyi gudu  ba?

    Idonshi nakan jaridan dan haka ta  murguda baki tace nayi?

    Toh irinshi zakiyi, idan kuma kikabari har mukaje gida bakizo ba, zan kirga mintocin da kika kara duk minti 5 yana da bulala 15, be jira mezatace ba yace usman muje"

    Figar motan sukayi kankace me suyi nisa sai kellin motar take hangowa"

    Cije lebe tayi sannan tace lallai abokin yayan nan bakin mugune har yafi yaya mugunta idan ba samun guri ba daga zuwanka bakunta zakace zaka dake ni ko gidan ma bakaje ba?

    Cafdin ta fada afili wlh bazan tsaya ka dakeni ba idan ko ya dakeni da abba zan hada su"

    Juyawa tayi ta fara tafiya lokacin data shiga gida ana kiran mangariba"

    Aharaban gidan taci karo dasu zasu masallaci"

     Abokin yaya taga ya kalli agogon dake daure ahannu shi sannan yaci gaba da tafiya batare daya kalleta ba"

    Koda ta shiga gida mama bata nuna fushinta ba"

   Dakinta ta wuce tayi wanka sannan ta dauro alwala Riga da siket ta saka na atamfa sannan ta saka babban hijjabi. ta tada sallah"

    Bayan ta idar ta wuce dakin mama"

   Tana shiga mamata tace ke kuma garinyaya kare ya tareki kinason kizama ballagaza ko?

    Shiru tayi dan haka mama taja tsaki sannan tace wuce Ki dauki abinci ki kai falon abban ku"


    Bata kawo komai a xuciyarta ba, ganinta abba zata ajewa abinci kafin ya shigo dan haka da karfinta ta shiga falon"

    Turus tayi lokacin da taga abokin yaya zaune akan doguwan kujera ya miki kafa fuwan shi"

    Cikin sauri ta aje abincin ta juya zata fita taji muryan yaya usman yace"

   Ke zonan?

   Dawowa tayi ta tsaya tana kokarin matso hawaye".

    Jitayi ya sake cewa *JAMAL* gata"

   Kaman jira yake ya juyo ya sakko da kafan shi kasa sannan yace kina da bulala 30"

 
     Kallon su kawai take dan ita gani take wasa suke zuwa can taga wadda yaya usman ya kira da suna *JAMAL* ya mike sannan ya saka hannu a aljihun gaban gaban wandon shi daidai guiwa ya ciro wata zafgegiyar bulala sannan yace daga zanin Ki.....






   
   Heart Beat
*Mmn Yazeed*
.​
[12/3, 8:37 AM] ‪+234 803 308 6255‬: 💗💝💝💗
​*BUGUN ZUCIYA*​
   ( ​Heartbeat​)

                   💓💝💗
                        💗           

💓💝💗
​By​
     💗
    ​​*Fadeela Lamido*




*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*




   
  1⃣7⃣ to 1⃣8⃣





📙 Na daga zani ? Lailai wannan dan rainin hankali ne aiko yaya betaba cewa na daga zanina ba, bare wani katon banza"

   Muryan yaya usman taji yana cewa wai bada ke ake mgn ba?

   Karya murya tayi sannan tace ai ba zani bane siket ne"

    Abokin yaya taji yace koma menene ki dageshi sama"

    Cikin sauri ta kalleshi saidai shi ba ita yake kallo ba"

    Mikewa yaya usman yayi ya fice dan haka Asmau taita zubawa abokin shi harara"

    Zuwa can taga ya fara tahowa yanazuwa daidai inda take yasa kafa ya kwasheta"

    Ganinta kawai tayi akasa cikin sauri ta fara kokarin mikewa amma ina jitayi kwankwasonta ya rike"

    Daker ta iya dago kanta ta kalleshi daidai lokacin daya dago hannu ya sauke mata mari"

   Innalillahi wa inna ilaihir rajun'un ta fada da karfin saboda zafin marin ya shigeta, zaki daga ko bazaki dagaba?

   Wlh zan daga arude ta Kwaye zanin har zuwa guiwa, tare da tsiyayar da hawaye"

    Bulalan ya daga sannan yace idan kinga dama ki kirga, dan ni ba kirgawa zanyi ba, kuma idan kika sosa bandashi alissafi"

    Fukanta cike da hawaye ta kalleshi acikin zuciyanta tace lallai wannan bakin mugune so yake yaga karshena, nan danan taji wata dakiya tazo mata, dan haka ta tsaya cak"

    Kin shirya?

  Eh tafada tana kauda idonta gefe"

    Bulalan ya daga yaita zula mata tuntana daurewa harta kasa taita zuba uhu"

    Shiko *JAMAL* kaman kara zugashi take har wani tsalle yake yi"

    Goggo tani ce tajiyo uhunta tundaga cikin gida harda gudunta ta nufi idan take jiyo sautin kukan daker ta kwaci ma,u ahannun sa"

    Hargun mama goggo tani takai ma'u tanaci gaba da korafin cewa adaina mata irin wannan dukan haka kwanaki usman ya  mata dan banzan duka kartaxo ta saba da duka"

    Mama batace komai ba mikewa kawai tayi tabar dakin"

   Nan ma,u ta kwanta tanajawowa *Jamal* Allah ya isa acikin zuciyarta"

    Ko ina ajikin ma,u ciwo yake dan yau abin ya mata yawa ga wahalan da *Duna* ya bata gana wannan dan iskan abokin yayan"

 
       *****


  Washegari ma haka ta tashi batajin kwarin jikinta dan haka batace zata makaranta ba"

    Misalin 11 tayi wanka ta danji dadin jikinta, falon Abba ta wuce acan ta samu mama"

      Gaban abba ta zauna ta tankwashe kafa sannan ta fashe da kuka"

   Nan danan hankalin Abba ya tashi, zaman shi ya gyara tare da kura mata ido sannan yace"

   Mamana waye ya taba ki?

   Cikn kukan tace ba yaya usman bane yacewa abokinshi wai banajin, shikuma kawai sai ya ciro bulala ya hau dokana"

   Abokin nasa?

    Eh Abba"

   Duka fa kika ce mamana?

   Xanin ta ta fara dagawa tare da fadin eh abba kagama gurin"

   Babban mgn Abba ya fada bayan yaga inda jikin ma'u yai rudu2"

   Mikewa yayi sosai sannnan ya daga waya ya kira usman"

   Cikin Monti 15 suka iso, dukka su jallabiya ce ajikin su fara kar"

   Tunkafin su zauna abbba yake fadin a'a wanake gani kaman *Jamal*"

   Mumurshi kamal din ya saki yana shafa keya yake fadin nine abbba"

     Bayan sun gaida abbba hira suka hauyi,  dan haka ma'u ta Kule"

     Mikewa tayi tana kokarin tafiya Abba ya dakatar da ita sannnan yace"

   Mamana kinga wannnan sunan shi Jamal yayanki ne shima, nida mahaifin shi tare mukayi wasa, dan haka yadda usman yake da daman hukuntaki shima yana da dama kijji ko"

   Tana barin falon ta fara kunkunai kai tsaye ta wuce dakin mama dan daman  tuni ta bar musu falon, zama tayi  tare da share guntun hawayenta sannan taci gaba da kunkunan ta"

    Mama na gefe tanajinta jefi jefi tana tsintan abinda take cewa, zuwa can tace"

    Kee!!!! Tashi kibani guri, haka kurun zakizo kisani agaba kinamin mita toh me kikeso nayi rama miki zanyi kome?, yariya banda fitsara ba abinda kikasa agaba ke wacece da baza'a dakeki ba?, to kici gaba kece zakisha wahala"

    Dahaka mama ta fice tabarta adakin"

    Itama mikewa tayi tabar dakin"

     Tundaga ranan asmau bata sake zuwa makaranta ba har wani satin ya zagayo, gashi kewan deen ya dameta, dan tasan yanzun har ya gaji da zuba ido"

 
      ***



Yau ta kama asabar dan haka tunda wuri ma'u tayi sallama ta fito"

   Saidai tana fitowa taci karo dasu yaya suna kokarin shigowa"

    Dauke Kai tayi taja gefe sanan tace ina kwanan Ku murya ciki2"

     Yaya usman ne kawai ya amsa amman jamal gaba yayi, harta kusa fita taji jamal na cewa usman, kunabin bayan yariyar nan Kuwa....

   Daidai lokacin suka sha kwana dan haka bataji amsan da yaya usman ya bashi ba"

    Tana tafiya tana waige dan gani take kaman Jamal zai biyo ta"

     Hango deen akofar gida shine yasata ta manta komai tundaga nesa ya sakar mata murmushi itama mayar mai tayi tare da sunkuyar da kanta kasa"

    Tana isa gaban shi taja ta tsaya tare da kara sunkuyar da kanta kasa"

    Babu abinda deen yake banda kallonta acin tuhuma ya dago fuskanta sannan yace"

    Me yasame ki kwana 2 ?

    Shiru tayi tana kara tsurawa kafarta ido"

    Girgiza kai yayi sannan ya cije lebensa na kasa Yasa ke daga ido ya kalleta cikin bacin rai yace"

     Yayan kin yasake dukan ki ne?

    Kanta na kasa ta girgixa kai"

   Kanshi ya daga ya kalli sama sannan yace yasin zanyi rashin mutunci wlh, fuskanki ya nunamin an cuceki kuma kina cikin bacin rai wai wanene wannan yayan naki? a ina zan sameshi ?

    Nan danan hawaye ya fara zubo mata dan bakaramin takaici takeji ba, haka kurun daga zuwan shi zaisa bulala ya zane ni"

     Murya kasa2 tace ba yayana bane, abokin shi ne"

    Abokin sa ? Idon shi daya ya rufe sannan ya karkata dayan yace dukan ki yayi?

    Hannu tasa ta share hawayen daya zubo mata sannan tace eh"

    Uban wanene ya bashi iznin ya dake ki?

    Bata iya cewa komai ba illah kukanta daya karu"

   OK shikenan dena kuka kingane?, ban ni dashi zan nuna masa daya tabaki gara yaje ya tari babban mota, haduwan mu bazaiyi kyauba naratse sai uwassa ta kasa gane shi"

     Yana mgnr ne yana daga hannuwan shi tare da karkace baki"

     Ganin inda yake fada yana tiriri yasa ma'u jin dadi ko banza tasamu wadda zai kwatan mata enci, amma tafison deen yayi abin cikin sirri ba baro baro ba dan batason kowa yasan shi arayuwar ta"

   Dago kanta tayi sannan tace bari na shiga makaranta idan antashi zan shigo nagaida ummi....

   Batajira me zaice ba ta fara tafiya tana jiyo muryan shi yana cigaba da babatu"

    Ko a makaranta batayi karatun kirki ba, kawai tunanin hanyan daukan fansa take"

     Zuwa can tunanin duna ya fado mata, tabas duna kadai ya ishi jamal amman idan deen ne duka zasu masa dan suma suna takama da karfi, karshema kila su kamashi, amman duna zai iya basu whl batare da sun san waye ya turoshi ba"

     Kwashewa tayi da dariya sannan tace inama ina gurin inga ya zasu yi?

     Takarda ta samu ta fara rubuta yadda takeson abin ya kasan ce, tana cikin rubutun aka tashi tsayawa tayi ta karasa sannan ta fito"

    Lokacin da tafito babu sauran dalubi amakaranta duk sun fita"

    Gabanta ne yayi mummunan faduwa sakamakon hango Jamal tsaye shida baba idi"

    Batasan me suke cewa ba, tana kokarin fita taga jamal ya wuceta"

   Abakin makarantar taga motar yaya usman, budewa Jamal yayi ya shiga, har sun tada mutar yaya usman yace shigo mutafi"

    Wani haushi ne ya kamata, tasan duk shirin jamal ne, bayan ta zauna suka fara tafiya banda masifa babu abinda yaya usman ke yi, Jamal ko kauda kansa gefe yayi ya bude jarida"

    Ma,u ko hankalinta yana kan dakalin da deen yake zama, yana nan zaune sai raba ido yake"

    Suna zuwa daidai inda deen yake ta saka hannuta ta widow motar sannan ta wurgawa deen takardan data rubuta"

    Akan jikin shi ya fada, tana kallon deen ya dauka sannan yabi motar da kallo"

    Sun gota gurin kadan taga Jamal ya rufe jaridar hannun shi ya aje agefe, sannan ya cire glass din dake idon sa"

    Waigowa yayi ya kalleta cikin ido sannan yace"

   Usman koma baya....





 Heart Beat
*Mmn Yazeed*​
[12/3, 8:37 AM] ‪+234 803 308 6255‬: 💗💝💝💗
​*BUGUN ZUCIYA*​
   ( ​Heartbeat​)

                   💓💝💗
                        💗           

💓💝💗
​By​
     💗
    ​​*Fadeela Lamido*




*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*




   
  1⃣9⃣ to 2⃣1⃣





📙📙 Ahankali usman ya koma baya, kusa da dakalin deeni Jamal yace yayi"

     Hannu ya mika ya dauki glass din shi ya maida a idonshi sannan yace"

    Ke! Sauka ki karbo dakardan da kikajefa"

     Idanuwa ta fito dasu waje zufa taji yana karyo mata, kallo gurin tayi taga deen ya daga bakin shi sama yana fito"

    Jamal ya sake cewa ko bakiji abinda nace ba?

    Jikinta har rawa yake ta bude motar ta sauka, daga gefen dakalin duna ta hango wata takarda ko kallon inda deen yake batai ba ta tsuguna ta dauka, harta shiga motar tanajin fiton deeni"

   Usman ne ya karbe ta kardan ya bude babu komai aciki, tsaki yaja sannan yace kai manga kana da matsala wlh"

    Ko kallon shi beyi ba yace kaidai muje kawai, kaima ai matsalan gareka"

    Itako ma',u tunda ta dauko tasan ba ita bace, har suka isa gida babu wadda yace uffan"

       ***

 Da yamma tana zaune adakinta tunani ta shigayi ta yaya zata bullowa al amuranta"

   Hakika deeni yana matukar burgeta kuma da bi'un shi suna sata nishadi, amman idan ta tuna abbanta gabanta na faduwa"

    Koda atunanin ta bason deeni take ba, amman tana tsoron ranan da abba xaisan tana mgn da deen harma tana shiga gidan su, alhanin ya gargadeta daga makaranta ko gidan dada be amince taje ba"

   Hawaye taji yana zubo mata hakika batason bacin ran abbanta kuma tanason ta masa biyayya amman kuma tanajin deen ajikinta kuma tanaso kasancewa dashi akoda yaushe, har tanaji inama su zauna gida daya taita kallon shi harta gaji"

     Murmushi tayi lokaci da ta tuna yadda deen yayi data gaya mishi an begeta, tabas da zatabawa deeni dama da yayi banna komai girman mutum dan ya duramai zagi bawani abu bane, ji inda ya takarkare agabana yana cewa zaici uwar yaya, wata kila ya manta cewa uwarmu daya"

     Wata zuciyar ce tace ke ba mantawa yayi ba yana sane ko kin manta yadda yayiwa dada?

   Kwashewa tayi da dariya har tana rike ciki kai gsky dada matsuraciya ce, dagajin zance sara ta ware kafa amman da anyi mgn tace kafanta na ciwo*


     Dariya take sosai har da hawaye, da karfi taji anturo kofar, mama ce kallo tabi ma'u dashi sannan tace toh wai kodai mahaukacin kare ya cijeki ne?, mutum shi kadai yaita dariya adaki"

    Gintse dariyarta tayi sannan tace mama dada fah na tuna"

   Dada ?  Ke banason shashanci kinji ko, kiyi hankali  da kanki ba kowa bane keson dariya dallah ni tashi ki kaiwa su yayki abinci'

  Hade rai tayii  sannnan tace mama ni gaskiya nagaji da ganin su agidan nan waishi yaya meyasa  baazai kaishi gidan shiba??

   Ke tashi kiji bansoo. Surutun banza

   Mikewa tayi ta fara tafiya tana. tana  mgn ahankali"

   Binta da kallo. Mma
Sannan tace me kike cewa?

   A,a mama daman cewa nayi kodai Anty fa'iza tayi yaji ne?

    Cikin takaici mama tace bani da lbr amman idan kije kina iya tambayo shi"

    Bata sake cewa komai ba ta juya ta fita dan tasan mama gatse ta mata"

   Kwance ta same su afalon abba sunyi wani shabe shabe dasu, duk su biyun jikin su babu babu riga dan haka batace zata tsawaita kallon su ba"

    Jarida ce ahannun Jamal kaman yadda ya saba yayin da usman ke rike da waya yana dannawa"

    Ajiye abincin tayi ta juya zata tafi taji waya na kara

      Harta kai bakin kofa taji Jamal yace Haba Momy kiyi hakuri wlh wani abu ne ya tsaidani, amman gobe da wuri zan taho"

     Yadda Jamal ya kashe murya yana shagwaba abun yayi matukar bata mamaki dan haka taja ta tsaya tana jiran taji me zai sake cewa"

    Muryan yaya usman taji yace ke me kike jira"

    Azubure ta fice adakin"

    Koda ta koma daki addu,a taitayi Allah yasa momyn shi ta matsamai ya tafi gobe, dan wannan bakon gundura ne"

   Washegari da safe  bayan tayi shirin makaranta ta fito ta samu mama sai hada wasu kaya take"

     Cike da zumudi tace mama wannan kayan fa?

    Idon mama akan kayan tace wlh Jamal ne be tashi gayamin  zaitafi gida ba saiyau da safen nan, shine zan bashi turaren nan ko kyauta yayi dashi"

    Kasa boye murnanta tayi  tace ai gara ya tafi"

    Mama batace mata kala ba harta fice"

    Cikin farin ciki ta nufi mkrnt tanaji azuciyarta daga yau zaman kunci ya yaye"

    Tana daf da isa kofar gidan su deeni ta hango karnuka guda 3 sai shawagi suke"

     Ja tayi ta tsaya tare da dafa kirji, ido ta sake zuba musu manya2 karnuka ne amman duna duk ya fisu girma"

     Ahankali ta fara takawa ta koma lungun da kawarta zainab take bi dan bakaramin tsoron duna take ba"

         ***


Shiko Jamal karfe 10:45 ya mike yacewa usman bari naje wani guri na dawo"

    Cikin mamaki usman yace kadai CE natashi muje"

  A'a bana bukatan rakiyan kowa, ni daya zani"

    Mamaki ne yasake kama usman dan tunda yazo garin nan kusan satin shi 2 be taba cewa zai fita shi kadai ba sai yau"

    Murmushi Usman yayi sannan yace toh adawo lfy Allah ya tsare, key din motar sa ya mika masa amman sai yaki karba yace da kafa zashi"


   Makarantar su ma'u ya nufa yana tafe yana shirya muguntan dazai mata indai ya sameta da laifi"

    Koda ya hango karnnuka na shawagi be kawo komai azuciyan shi ba, dan ya saba ganin karnuka iri2, dan haka kanshi tsaye yake tafeya tare da neman inda zai labe yaga wucewan ma'u idan ma wani abu take shiryawa yau zai gani"

   Shiko deeni yana zaune kan dakalin da ya saba zama ya rufe ido tare da dage hanci sama"

   Kan Jamal tsaye ya nufi bita tsakiyan karnukan yana daf da shiga cikin su yaga sun haukace kaman suna fada da junan su, duk idan yaso be ya wuce nan suke dawowa suna kawai junan su rikici"

    Jamal be tsorata ba acikin zuciyan shi yace wadan nan wasu irin yan iskan karnuka ne"

    Daure fuka yayi sosai yayi kansu gadan kadan tare da niyan idan suka kawo mai wargi zai kai masu duka"

    Wata muyar yaji daga gefen tana cewa dan durin uwar mutun ya tabamin kayana yagani"

    Juyawa yayi ya kalli gurin da yaji mgn mutun ne zaune kato meji da karfe Kuma  daganin shi bayaji dan almun rashin ji sun bayana agareshi haka ne ya nunawa jamal shine mamallakin karnukan amman saidai kaman bashi ne yayi mgnr ba dan idon shi rufe yake"

    Karnukan ya kara kallo har yanzun sunan a inda suke dan haka ya daga murya yace "

   Ai sai kazo ka tattara kayan naka dan inason zan wuce"

    Baki deeni yasake dagewa sama yafara fito" dan haka Jamal yasa kafar yayi ball da daya daga cikin karnukan"

  Akuje duna ya taso ya yi kan jamal yana kaimai cizo tare da yakushi, saidai baya kawaiwa jikin Jamal din domin fada da kare ba sabon abo bene awajen shi, da duna ya kawo mai cizo yake kaimai duka"

    Ana haka aka tashi yan mkrnt, suna ganin abinda ke faruwa suka watse wasun su sunbi lugu wasuko makarantar suka koma, mau ko wani logu ta rabe tana lekowa tana komawa acikin zuciyanta tace kai Jamal akwai maye"

   Jikinta ne yayi sanyi lokacin da ta hango yadda jamal ke kaiwa duna duka, ga deen zaune ya rufe ido kaman me bacci hawaye taji yana zubu mata shikenan Jamal zai gama da duna ya dawo kan deeni tunda ciwon baccin shi ya motsa, jitayi kaman ta tashe shi dan tasan babu yadda za'ai idon shi 2 ya bari ana jamgar masa duna"


   Kuka take sosai hawaye shabe2 zuwa yanzun ta fara tausayawa duna itace tajamai gashi Jamal zai kashe abanza"

     Wani irin kuka duna ya fara almar yana shan wahala, yana fara kukan taji deeni yayi wani irin fito me kama da mgn, nan danan duna ya haukaci tare da wani irin haushi me firgitarwa yayi kan jamal akan damtsen shi ya kafa bakin shi saiga jini yana zuba"

    Hannu Jamal yasa ya danne gurin hakan yaba duna daman cigaba da cizon Jamal akafan shi dole tasa Jamal ya sake uhun da be shirya ba, tare da kokarin guduwa"

    Daidai lokacin ummi ta dawo daga cefane afirgece ta saki kanyan miyan sannan tayi kan duna tana kai! Kai!! Ja baya duna yayi amman har yanzun yana gurnani tare da kunbura wuya"

     Ma,u ko banda dariya babu abinda take saidai taso ace duna yabi Jamal aguje"

     Tana cikin wannan tunanin taji duna ya sakeyin fito aguje taga duna ya wuce sauran karnukan nabin shi abaya "

      Sai alokacin mutanan unguwan suka fara fitowa, deen ko mikewa yayi ya shige gida"

    Allah wadai mutane suketayi da halin deeni yayin da wasu daga ciki suka rufan ma ummi da hayaniya cewa tajawa danta kunne"

     Wasu dadtawa ne su 2 suka saka Jamal amota suka nufi asibiti dashi"

   Cikin gida ummi ta nufa tana share hawaye, hakika babu dade ace danka bayaji tabbas ta sani duk unguwannan babu me irin dabi,un deeni kuma tasani kuskure ne da tayishi tun abaya ta manta cewa ice tun
yana danye ake tankwara shi, afili tace babu komai zanci gaba da addu'a Allah ya shirya min shi"

     Koda tashiga gida batawa deen mgn ba wuceshi tayi tana cigaba da share hawaye"

  Kallonta kawai yayi ya kyauda ido, daidai lokacin Asmau ta shigo fuskanta dauke da murmushi"

  Shima murmushi yayi sannan yace zoki zauna"

  Girgixa kai tayi tace sauri nake amman yaya akayi kasan Jamal?

     Murmusawa yayi sannan yace ai jiya daku ka wuce na kare musu kallo na gane yayaki ne ta kama dake dana gani"

    Shiru sukayi zuwa can tace yaya shamsundeen wai dan Allah meyasa kake bacci akofar gida?

     Murmushi ya sakeyi sannan yace sabo da bana samon bacci da dadaddare"

     Cikin mamaki tace toh meyake hanaka baccin?

    Cikin sauri ya jawo hannunta ya hada da nashi sanan ya kafeta da ido yace tunanin Ki ke hanani sukuni harna kasa bacci

     Tunani na kuma🙄?, dama kaima kana tunani na?

     Kema kina yin nawa ne?

    Cikin sauri ta girgiza kai, tare da fadin a'a"

   Karya kikeyi Asmau kinayi na tabbatar abinda nakeji kema kinaji"

   Hannuta ta janye sannan tace zan tafi, kar aga na Dade"

    Karajan hannuta yayi sannan yace toh wani tukuici zakibawa duna"

    Shiru tayi zuwa can tace to ka fadamin abin da yake ci gobe na kawo masa"

    A'a bayason abinci, goben idan kinzo zan nuna miki yadda zaki masa"

    Aranan saida deeni ya rakota har kusa da gida, suna tafe suna hira , yau ma'u jitake kaman karsu rabo da deeni, koda suka rabo sai waiwayen shi take"

    Shima kasa tafiya yayi yana jira wai sai ta shiga gida" darker suka hakura da kallon junan su"


    Tana shiga gida tasamu mama hankalinta tashe ko tambayan ina ta tsaya batayi ba tace"

   Asmau Jamal ne ya buguwa usman waya wai yayi hatsari tun dazun fah, gashi har yanzun basu dawo ba"

  Cikinta cike da dariya tace hatsari kuma??

    Kafin mama ta bude Baku suji tsayowan mota arude ummi tayi waje, yayin da asmau ta shige daki dan tasa bazata iya boye dariyarta ba"






    *Mmn Yazeed*​
💗💝💝💗
​*BUGUN ZUCIYA*​
   ( ​Heartbeat​)

                   💓💝💗
                        💗           

💓💝💗
​By​
     💗
    ​​*Fadeela Lamido*




*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*



Dedication 👇🏻
*Firdausi Sodangi*😘



     2⃣2⃣ to 2⃣4⃣




💝💗 Tana shiga daki ta fashe da dariya bakin window taje ta tsaya tana kallon yadda Usman ke kokari tallafu Jamal"

    Gajeren wando ne kawai ajikin Sa, kafan shi duk 2 nade suke da bandeji haka damtsen hannun shi na dama"

     Saida taga shigowan su sannan ta koma bakin gado ta zauna taci gaba da dariya tare da share hawayen mugunta"

        Bayan usman ya kwantar da jamal akan gadon dake dakin dake kusa dana abba, gefe gadon ya koma ya zauna sannan yace manga yaya akayi ka tsaya kare yacije ka?

     Ido ya runtse dan babu halin bude jarida"

    Binshi da kallo usman yayi sannan yace ina mgn kayi shiru"

   Cikin fada yace dallah Malam karka dame ni"

   Shiru usman yayi yana tunani zuwa can yace to kodai Karen daya tsare asmau ne ranan ?

   Bansani ba, nace maka kabar mgn sai wani nanatawa kake kare2 salon wani yazo yaji kuma"

   Toh meye idan anji uban waye yace ka tsaya kare ya cijeka, wlh ka bani mamaki Dan Allah ji inda ya maka kaca2"

   Kaga usman banaso ka rabu dani kawai"

   Mikewa usman yayi ya fice dan abin takaici yake bashi"

    Mama ko tayi tayi da asmau taje ta gaishe da Jamal taki zuwa, tanajin yadda mama ta takarkare tana gayawa Abba wai yau Jamal ya auna arziki"

     Dariya ce ta kwace mata taita tuntsurawa dan haka daga mama har Abba suka juyo suna kallon ta"

     Cikin fada Abba yace wanne irin iskanci ne wannan?

    Nan dan ta daure fuska tare da sukuyar da kanta kasa"

   Abba ne yaci kaba da cewa kina hauka ne, yaya ana mgn Mutun yayi hatsari Ki kama dariya"

    Mamace tace ai yanzun dabi'a data fara kenan ita kadai ma saikaga tana dariya, narasa gane kanta, Jamal ko Daman ta tsane shi wlh ina kula da ita tunda nace mata yayi hatsari annashuwa ta cika fuskanta"

    Fada yaita mata tun yanayi cikin fada har ya dawo nasiha akarshe ya kara da lallashi"


    Kwana 2 jamal ya fara samun sauki, dan haka yau Usman gida yake shirin tafiya dan matar sa ta dawa ta dawo tun ranan da abin ya faru"

   Jamal na zaune akan kujera yayin da usman ke zaune agefen shi"

    Usman ne ya kalli damtsen hannun jamal yace kai amman gsky karan nan ya iya tsiya toh wai ta bayanka ya biyo ?

    Kwashe duk yadda akayi yayi ya gayawa usman sanna ya kara da cewa kasan Allah saina naga uban da ya tsayawa mishi"

     Usman ne yace kana nufin karan yafi irin karnukan mu horo"

    Guntun tsaki Jamal yaja sannan yace wannan fa umarni ake bashi kuma ni tunda nake bantaba ganin kare me zafi kalan shi ba, amman na dakeshi sosai na tabbatar inda nai jiya shima saiyayi jiya dan dukan dana mushi banzaci zai iya tashi ba bare har yamin wani abu, kuma ni fa bawai nabar mgn bane"

    Aidama ko kanarta ni bazan bari ba abinda yasa ban daga mgn ba sabo da naga baka son asani"

    Eh banaso"

 Towai saboda me?

  Haba usman ina Sonja aga kare yamin haka?

    To ai tsautsayi ne ko?

   Shiru yayi zuwa can yace nifa sabo da wannan yariyan ne banason asani, kartazo ta raina muta ne

   Kallon shi usman yayi sannan yace au wai Asma'u?

    Ita, kasan yariyar ba kunya kareta ba kuma akwai wani abu da nake nazari idan na tabbatar zan gaya maka"

        ***

 Washegari ta kama alhamis dan haka yau babu makaranta ma'u na daki tana ninke kaya taji kiran mama"

    Bayan taje mama fada taita mata akan kin zowa gaida Jamal datayi, haba asma'u wanne irin zuciya gareki ace mutun agidan ku yayi hadari Ki kasa zuwa ki gaida shi, haba asma'u ke bakiji dadi bama daya nuna yadamu da lamarin ki ?

    Nan danan ta fara matso hawaye tare da fadin mama hakanan fah ya zanene saboda tsabar cin zalli wlh na tsane shi kuma idan Allah ya yarda bazai gama da duniya lfy ba"

   Ah, ah ah babban mgn Asma'u kanki daya kuwa? Toh idan kece uwarshi saiki hanashi gamawa da duniyan lfy"

    Wucewa mama tayi ta barta aguri, zama tayi taita kuka domin ita harga Allah bata kyaunar ganin Jamal, bata tabajin ta tsani wani ba kaman yadda ta tsaneshi"

    Har yamma mama bata sake mata mgn ba koma ta mata bata amsawa
 
 
    Ganin haka Yasa ta mike ta nufi dakin da Jamal yake tayi sallama"

     Daker ya amsa bayan ta shiga ta dan rage tsayonta sannan tace sannu ya jiki?

     Banza yayi da ita harta gaji da durkuson ta fara kokarin mikewa"

     Haka ake gaisuwa sannan saiyau kikasan bani da lfy ?

    Shiru tayi tare da turo baki"

    Shiru shiru zuwa can ta waiga daga yana bacci , zabura tayi ta mike harta taba kofa yasake cewa idan kika fita ranki zai baci tambaya nayi kuma inason kibani amsa"

     Shiru tayi taki mgn shikuma ya dage dole tayi mgn, ahaka Usman ya shigo ya same su"


    Murmushi usman yayi sannan yace kona koma ne?

   Hararan shi yayi sannan yace shigo mana"

    Bayan usman ya zauna Jamal ya kalleshi yace wai yariyar nan ajinta nawa?

    Usman ne ya waigo yace ke ajikin Ki nawa ?

    5 tafada batare da ta kallesu ba

sauraki shekara  daya kenan?

   Eh ta fada tana share guntun hawaye"

    Ganin inda take nuna alaman gajiya Yasa Jamal yace tashi ki tafi , wawiya dake kawai"

   Tana fita Jamal yabi bayanta da kallo sannan ya juya yacewa usman usman wannan yariyar yaushe zaku mata Aure?


    Shiru usman yayi yana nazari, zuwa can ya hada fuska sannna yace"

    Munyi mgn da Abba kwanaki yace data yi sauka zaiyi mata Aure, kaga kenan bazai wuce nan da shekara 1 ba"

   Kuna nufin bazata karasa karutunta na ban garen boko ba?

  Eh gsky kozata karasa sai adakin mijinta, saboda wannan dalili dana gaya maka"

   Shiru Jamal yayi zuwa can yace amman da kun bari ta karasa saboda yanzun zamani ya canza kuma bakowanne namiji bane zai yadda matarshi ta tafi makaranta,  kaga kamarni bani da ra'ayin mace tana gida na kuma tanazuwa makaranta, saboda na sani inada kishi sosai"

   Girgiza kai usman yayi sannan yace ina aiko ni bana goyon bayan Asma'u taje Jami'a idan mijin da zata aure be amince ba shikenan wadda ta samu Allah ya amfana"

    Shiru Jamal yayi tare da rufe ido, ganin haka usman ma ya kwanta agefe, sun kwashe kusan minti 30 ahaka, Jamal ne ya kira usman batare da ya bude ido ba"

    Waigawa usman yayi yayi ya kalleshi sannan yace yaya akayi ?

    Daman tambayan ka zanyi kun mata miji ne?

   Wani haushi ne ya kama usman nandanan ya hade rai sannan yace Eh ammata wani abu ne"

   A'a tambaya ce kawai, jamal ya fada yana kokarin tashi, akwatin shi ya dauko ya fara hada kayan shi yana zuba kayan yana fadin gida zani gobe"

    Gobe kabari mana sai ka kara warwarewa"

   
     A'a ni gida zani mezan zauna nayi?

   Dacan me kakeyi?

   Cikin fada yace dalla gafara Malam karka dameni, ubana ne kai daxaka tareni da tambayoyi?

    Mamaki ne ya kama usman, cikin shi cike da dariya yace Allah ya baka hakuri"

    Jamal bece komai ba yaci gaba da hada kayan shi"

       ****


  Washegari Jamal yayiwa su mama sallama, Abba yaso ya kara kwana biyu amman Jamal ya dage"

    Tare da usman suka fito har sun shiga mota usman na kokarin tayarwa  Jamal yace usman dan Tsaya...

    Tsayawa usman yayi yana kallon jamal"

   Basarwa Jamal din yayi sannan yace ko kuma muje kawai"

    Usman bece komai ba ya tada motar har ya fara tafiya Jamal ya ja tsaki sannan yace wai *Husna* batanan ne ?

   Sarai Usman ya gane wayake nufi amman saiyace wacece *Husna* kuma?

    Cikin dakewa yace *Asma'u* nake nufi"

   OK kasan dayake babu me kiranta da *Husna* sainaji abin yamin banbarakwai yana mgnr ne yana kara waya akunne, zuwa can yace mama dan Allah turo mana *Asma'u*"

   Usman na sauke waya ya juya ya kalli jamal, sai wani daurewa yake yana wani basarwa, dariya ce taso kama usman Amman saiya cije yace ga *Husnar* nan zuwa"

   OK Toh daman inaso ne nadan ja kunnen ta"

   Daidai lokacin Asmau ta fito dan haka usman ya bude motar yana kokarin fita yace eh gsky haka yana dakyau"











   Heart Beat
*Mmn Yazeed*​

💗💝💝💗
​*BUGUN ZUCIYA*​
   ( ​Heartbeat​)

                   💓💝💗
                        💗           

💓💝💗
​By​
     💗
    ​​*Fadeela Lamido*




*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*




     2⃣5⃣ to 2⃣7⃣





💞💝 Gefe ya koma ya zauna, yana mamakin halin jamal

  Itako  Asamau fuskan nan murtuk ta tsaya agefen da jamal ke ciki sannan ta turo baki tace gani "

    Daure fuska yayi murtuk kaman be taba dariya ba sannan yace ni sa'an wasanki ne zaki tsaya daga nesa kina cemin wani gaki ?

   Bata rai tayi kamar zatai kuka sanna ta matsa kusa da widow motar tana cigaba da turo baki"

    Fuskar shi adaurai yace nayi ciwo harman warke bakizo kika duba ni ba, yanzun gashi zan tafi bakizo muyi sallama ba ko?

    Rasa inda mgnr shi ta nufa tayi dan haka tamai shiru tana wasa da hannunta"

   Ajikinta taji kallonta yake cikin sauri ta dago ta kalle shi"

     Sauri yayi ya dauke idon shi sannan yace *Husna* bazaki min mgn ba ?

   Batace kala ba , ganin lokaci na tafiya Yasa Jamal yace shikenan nizan tafi gida ki kula da kanki, kuma ki rage son wasa, kinji ko?

    Kai kawai ta daga mai"

    Hannu yasa aljihun gaban rikar shi ya Ciro kudi ya kirga 20k ya mika mata"

    Hannu buyu tasa ta karba dan ta kosa tabar wajen, juyawa tayi da nufin tafiya taji yace *Husna* nacewa Momy na kina gaisheta ?

     Kaita sake dagawa sannan ta juya da sauri dan ta kosa ta daina jin muryan shi"

   Usman na Ganin wucewan asmau yatashi ya koma, aguje ya tashi motar yabar gidan"


   Asmau ko tana shiga gida ta mikawa mama kudin tace gashi nan yace nakawo miki"

    Tunkafin ta rufe baki mama tace karya kikeyi aini yabani nawa".

    Mama to nima na baki, ni banason komai nashi wlh yadda na tsaneshi haka na tsani duk wani abu daya shafe shi"

   Kai asmau nikam al'amarin ki yana bani tsoro, kin fiye naci da mitan tsiya, dan Allah kiyi hakuri kibar mgn yanzun dauki kudinki ki wuce ina ce dazun kikace nabaki 3k ?

    Em mama kibani amman ni wlh bazan bazanyi amfani da kudin shi ba"

   Mikewa mama tayi tare da fadin Allah ya shirye ki"


         ***


Tunda Jamal ya tafi ma'u ta saki jikinta kulum da wuri take zuwa mkrnt , sai ta fara biyawa gidan su deeni sannan ta wuce makaranta"

    Kuma da antashi break take kumawa sai kuma taji anbuga kararrawa sannan ta koma mkrnt"

   Shakuwa sosai sukayi da deeni, baya zuwa ko ina sai ya jira anta she su akamakarata, zuwa wannan lokacin kawayen ta rahama da zainab sun fahimci halin da suke ciki tsakaninta da deeni, dan haka dukkan su tsoron mu'ammala suke da ita, duk da cewa basu taba taranta akan mgnr ba amman sun san soyayya suke yi"

    Ahaka har suka kwashe tsoyon wata 8 zuwa wannan lokacin ma'u ta fahimci son deeni,
 Take Dan  haka shima deeni soyayyan asma'u yakeji sosai azuciyar shi, saidai babu fargaban komai azuciyan shi dan gani yake ko za azubar da jini saiya Aure asmau"

    Itako asmau anata bangaren tana fargaban kaimai deeni a matsayin mijin da zata aure domin tasan mawuyacin Abu ne Abba ya yadda da zabin ta, dan haka ta fara shiga damuwa"

       **

 Abba ne zaune cikin mota akan hanyar su ta zuwa gidan dada"

   Kallon asma' u yayi sosai yace mamana wai meke damunki kwana 2 ?

   Karya ta shirya ahankali tace babu komai abba kawai karatu nake dan munkusa fara jarabawa ga kuma saukan mu na tahowa"

    Har cikin zuciyan shi yaji dadi, fuskan shi dauke da murmushi yace"

    Allah ya taimaka mamana, saura wata 2 ko?

    Eh abba"


Murmushi yayi sannan yace kinga dakin gama sai Aure ko ??

   Zuciyarta taji ta bugu cikin sanyin jiki tace um um Abba ba yanzun ba"

    Kul mamana kar muyi haka dake, isha Allahu bazaki kara wata uku agida ba, Aure zakiyi mamana, meye amfanin zaman"

    Nan danan idonta ya ciko da ruwa bawai auren bane bataso deeni ne bata shirya kaishi gida ba"

    Baitai aune ba taji hawaye na zubu mata, hannu tasa ta sharewa Abba ne ya juyo ya kalleta sannan yace"

   Mamana kina kuka ne ?

   Shiru tayi tare da daura hannuwanta dukka biyu afuskanta"

   Kallonta abba ya sake yi sannan yace Asmau Ki kwantar da hankalin ki, karkiga wai dan har yanzun baki kawo kowa amatsayi wadda zaki aura ba, zaisa namiki auren dole, bani da niyar na aurar dake ga wadda bakiso, dan haka Ki kwantar da hankalin ki kinji ko?

    Sosai taji dadin mgnr Abba acikin zuciyarta tace haka na nufin duk wanda nake so Abba zai amince dashi, yanzun idan nakai mai deeni zai barni na Aure shi?

   Dahaka suka isa gidan dada, harta sauka ta shiga ciki Abba sai kallonta yake yana murmushi tare da godewa Allah da bashi yariya kimtsatsiya"

    ***

Jikinta babu kwari ta shiga gidan dada, idonta har sun fara tasawa almar tayi koka"

    Atsakar gida ta samu dada tana shara kai tsaye ta wuce daki"

   Bayanta dada tabi da kallo daidai lokaci da Abba ya shigo dada take fadin ita kuma wannan meya same ta"?

    Abba ne yace rabu da ita dada shirman miyace"

    Tabarma ya nufa ya zauna sannan suka shiga gaisawa da Dada, sun dan taba hira har ya bada lbrn yadda sukayi da Asmau "

   Cikin dariya ta mike tace inazuwa barin ganta"

   Kan gado ta sameta ta kwanta ta kifa ciki' ahankali dada ta Saka hannunta ta dagota sannan tace ke kanki daya kuwa ?

    Shiru tayi dan haka dada tace" to shike nan tashi Ki gayamin meye matsalan ?

    Tashi tayi da sauri ta zauna sannan tace dada idan na gaya miki zaki tai make ni?

   Me zai hana takwara?

   Dada ?, idan na fada miki bazaki fadawa Abba ba?

   Nan danan jikin dada ya haurawa ba komai ta tuna ba , sai Firdausi mgn da ma' u tayi yasa ta fara tunani ko itama ta kwaso abin mgn ne, dan haka batasan lokacin da tace babu meji takwara ina jinki"

    Hawaye ne ya zubo mata tasa hannu ta share sannan tace"

   Dada dan Allah ko abinda zan fada be miki ba, ki tai make ni kirufa min asiri"

     Naji naji Asma'u menene kike ta maimaita zance daya"

   Dada nifa deeni nake so"

  Tsaki dada taja sannan tace to dan wanan kiketa kunbiya2, wanene deeni?

   Dada baki ganeshi ba ? Shamsu fah na kayin makarantar m...

 
    Zaro ido dada ta yi tare da dafa kirji arikece tace kar dai kice min wannan tambadaden yaron?

   Cikin sauri Asma'u ta diro ta Saka hannuta duk biyun ta rufe bakin dada"

   Dada ko banda rawa babu abinda jikinta keyi salati take kokarin yi amman saboda rawan jiki fadi take"

  Kalu lahaula innalillahi La,ila ha'illahu......



Asmau kara rudewa tayi ta manta tsoron dada shiya harta fada mata"

   Tsugunawa tayi ta rike hannu dada tace dada dan Allah kiyi shiru haka ya isa"

   Ina rawa kawai jikin dada yake gaf2 idonta na kifkifyawa"

  Cikin matsan cin kuka tace dada yau dan nagaya miki damuwata shine kika rikece, dada idan ban gaya miki ba wa zan gayawa, kefa kika ce duk abinda ya dame ni na fada miki"

   Arikece Dada ta bige hannun asma'u tare da fadi ke dallah can rabo dani neman tsari nake"

    Toh dada ai ba daidai kikeyi ba kibari karkizo kiyi sabo"

   Kallonta dada tayi sannan ta saki salatin ta fara fadin"

Summassabila yassara....



  Kara danne bakin dada asmau tayi cikin rude tace dada dan Allah kiyi hakuri kar Abba yaji"

    Ina dada bata san tanayi ba cigaba tayi da addu,ai ta batare da tasan metake fada ba"

   Itama asmau rudewa tayi tare da kirgixa dada daker ta samu dada ta dawo cikin hayyacin ta"

    Kallo dada ta bita dashi tana share zufa zuwa can dada ta dage ta kwasa mata mari"

    Hannu tasa ta dafe gurin tare da runtse ido"

   Mikewa dada tayi sannan tace duk yadda akayi kinada wani ciwo acikin kanki, idan ma mafarki kike to maza ki farka, dan bazai taba tabbata ba"

    Cikin kuka asma'u takalli kofa sannan tace dada to kiyi shiru kar abbba yaji"

   Dallah can rufemin baki fitsarariya tir da halin ki, waye zaiso ya hada zuriya da irin jaraba inbada ke shasha"

    Ta inda dada take shiga batanan take fita ba, ma'u ko kuka take yi, tare da data sanin fadinwa dada"

    Dada ko rufe ido tayi taita masifa daga karshe ta kara fasa kuka"

     Saida sukayi me isan su sannan dada tace Asma,u kiyiwa girman Allah ki fita harkan Yaron nan, ni daman tunda na ganku tare kwanaki hankali na be kwanta ba, na firgita da ganin ku tare, wlh takwara ina gargadin ki karki yadda abbanki yaji wannan mgnr, kisan ba lafiyayye bane tun tuni akace zuciyar shi tana daf da bugawa"

    Kudundune kai asma,u tayi tana kuka ciki2, zuwa can ta dago kai tace shikenan dada naji nahakura, idan Allah yaso zan cireshi azuciyata, sannan dada dan Allah karki gayawa kowa"

    Cikin fada dada tace bazanyi shiruba asmau , idan nayi shiru na zuba ido wani abu kuma ya faru fah"

   Dada babu abinda zai faru namiki alkawari dada daga yau bazan sake kulashi ba"

   Yadda asmau ta marairaice ne tabawa dada tausayi, dan haka ta shiga mata nasiha"

   Da gsk jikin ma'u yayi sanyi dada ta kula da haka, dan haka bayan ta gama ita da kanta ta daga ma'u sannan ta share mata hawaye tace muje kar abban Ki ya gaji da jira"


    Tsaye suka samu  Abba ganin fitowan su yasa shi fadin da zanje na dawo ne"

     A'a karka batta tasata agaba ku tafi gida"

    Sallama yayi ya fice ma'u nabin shi abaya"

    Har suka isa gida tana share hawaye abba na kula da ita amman yayi kaman be ganta ba, a tunanin shi mgnr auren da yayi mata ne"

    Ranan ma'u bata runtsaba tunani yadda zatayi ta rabo da deeni take, amman duk inda ta juya saitaga bazata iya rabuwa dashi ba"

    Washegari ma babu mkrnt wuni tayi da tunanin deeni acikin zuciyan ta ta yanke shawaran gayawa deeni ya nemo masu mafita"

    Washegari ta kama asabar dan haka karfe 7:30 tayi sallama ta wuce mkrnt"

    Tundaga nesa take kallon gurin zaman deeni abin mamaki yau babushi aguri, mamaki abin ya bata dan kullum gurin take samun shi"

    Koda takai kofar gidan gurin ta tsaya ta kallah sosai sannan ta shiga cikin gidan"

    Ummi ta gani zaune ita da wata mata sai kuka take matan na lallashin ta"

    Arude tace ummi lafiya ?

 
    Ummi tana kuka tace Asma'u ankama auta, suntafi dashi"

   Ankama deeni ? Ummi waye ya kamashi? kuma me yayi?

    Share hawaye ummi  tayi sannan tace"

    Asma,u  bansan me yayi musu ba, muna cikin bacci mukaji sojoji cike da gida, kafin infito ma sunsa deeni amota, wasun su suna kaimai duka"

     Tsugunawa ma'u tayi ta fara kuka saida tayi me isarta sannan tace ummi babu wadda yabi bayan su?

    Sojuji ne fa asmau, kisan ba hankali suka cika ba kuma da alama badaga nan garin suke ba"

   Zama tayi dirshen taita kuka ranan bata iya zuwa makaranta ba, tana ganin lokacin tashi yayi ta wuce gida tana tafe tana kuka,

    Akofar gida sukaci karo da abba kallonta yayi yaga idonta jawur yace lfy?

    Abba cikina ne yake min ciwo"

    Cikin tausayawa Abba yace toh sannu maza ki shiga gida"

   Kaitsaye dakin mama ta shiga domin yau ta rasa inda zata tsoma ranta jikin mama ta fada sannan ta saki kuka meban tausayi"

   Jikin mama sanyi yayi dan bata taba ganin ma'u nayin irin wannan kukan ba, cike da damuwa tace asmau daina kuka ki gayamin me yayi zafi ?

   Cikin muryan kukan tace mama bani da lfy"

   Jawota mama tayi ta rungume dan yanayinta ya fara bawa mama tsoro, tana kwance ajikin ta tace menene yake miki ciwo?

   Bansani ba mama, wlh bansan abinda ke min ciwo ba"

   Shiru mama tayi tana kallon ma'u zuwa can tace"

    Asma'u idan akwai abinda ke damun ki kifada karkice zaki boye mana damuwar ki"

    Shiru tayi bata sake cewa komai ba tai kwance jikin mama jefi2 kana jin ajiyan zuciyarta"

    Ganin ta samu natsuwa yasa mama ta kalleta sannan ta jawo Wata leda akusa da ita ta daura mata ajiki"

   Duk da tana cikin damuwa da zumudin ta ta fara bude ledan, da kwalin waya ta faracin karo, jikinta babu kwari ta bude kwalin sannan ta ciro wayar, waya ce lafiyayya dadi taji sosai ajiye wayan tayi ta kara leka ledan takalma ne kafa 3 masu kyan gaske tare da turare masu tsada"

   Kallon mama tayi tace mama wannan kayan fah ?


  Naki ne yayanki ne ya kawo miki, yace agaidaki sauri yake aiki ne yakawoshi

  Yayana ? Mama wanene yaya na?

     ​


 
   Heart Beat
*Mmn Yazeed*​


💗💝💝💗
​*BUGUN ZUCIYA*​
   ( ​Heartbeat​)

                   💓💝💗
                        💗           

💓💝💗
​By​
     💗
    ​​*Fadeela Lamido*




*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*




    Na sadaukar da wannan shafin ga masoya *BUGUN ZUCIYA* aduk inda suke 👌🏻💝😘



     2⃣8⃣ to 3⃣0⃣





🏀 Yayan ki *Jamal*

Mikewa ma'u tayi da sauri sannan tayi jifa da ledan " bantawa tayi tacire wayar acikin kwali dan haka ta dauki kwalin ta buga da kasa" sai lokacin ta kula dan haka ta dauki wayar ta makawa bango"

   Ji kake tassss"

   Da gudu ta fita ta nufi dakinta ta fada gado tare da saka sabon kuka"


    Wato Jamal ne yaje har gida ya kama deeni ? Ko tantama batayi Jamal ne wani sabon tsanan shi taji axuciyarta ji take kamar ta kashe shi"

     Tashi tayi ta zauna yanzun meye abinyi ?

   Yaya zanyi inkubutar da deeni daga hannun Jamal


Mama ko mamakin hali irin na ma'u tayi sannan ta juya ta kalli bannan da tayi ta girgiza kai, cike da takaici ta fita adakin"

   Da misalin karfe biyu da rabi ma'u ta fito cikin shirin tafiya mkrnt yamma, kallonta mama tayi taga idonta duk sun kumbura cikin idonta jawur sun kankance, da alamar ma ko cire kayan makaratar batayi ba tunsafe, dauke idol tayi akanta domin al'amarinta ya fara bawa mama haushi"

   Saida ta turu baki tace natafi"

  Ko kallonta mama batayi ba tace adawo lfy"

     Kaitsaye gidan su deeni ta shiga, ummi nazaune ta tasa abinci agaba ta kasa ci"

    Gabata ma'u ta zauna ta bude sabon kuka, hankalin ummi kara tashi yayi, rufe abincin tayi sannan tace ki daina kuka Asma'u bakiga inda fuskan ki ta kunbure ba, mutaru miyi hakuri inada tabbacin auta na zai dawo gida domin nasan shiba rago bane, wannan tashin hakalin da kika ganni ci narashin tabbacin inda yake ne da rashin sanin halin dayake ciki amman da yardan Allah auta zai dawo"

    Dahaka ummi ta samu ta shawo kan ma'u, ta wuce makaranta"

    Da daddare Asma'u na kwance afalo tana cigaba da tunanin deeni badan tana tunanin kar asirinta ya tonu ba data ansa no Jamal agun yaya usman ta bashi hakuri ya sakar mata deeni"

    Tana cikin wannan tunanin taji sallaman yaya usman rufe ido tayi kaman me bacci, Allah2 take ya wuce amman saitaji ya zauna akujeran dake kallon nata"

   Zuwacan mama ta fito tana fadin ka iso?

   Eh naje gidan momy yanzun tacemin kina nema"

   Zama tayi sannan tace eh Daman Asma'u ce gatanan narasa gane mata, kwashe duk yadda akayi tayi ta gaya masa"

     Sannan ta nuna masa yadda tayiwa wayar da Jamal ya kawo mata"

   Cike da baccin rai yace mama bawani abinda yake damunta banda iskanci da sangarta, bataga ba,a dukanta ba kuma ai ba wuce dukan tayi ba, dan ubanta Jamal din sa'anta ne

     Usman na tsaka da fada Abba ya shigo, daga mama har usman sannu suke mai" amman abban yaki amsawa fadin yake ina Asma'u

   Toh fah mama ta fada azuciyarta domin indai taji alhaji ya kira ma'u da sunan ta toh akwai mgn"

    Itako ma,u tanaji Abba ya kira sunanta ta bude ido tare da sakkowa akan kujeran azuciyarta tace shikenan dada ta fadawa abba"

    Kusa da ita abba ya zauna sannan ya rike hannunta guda daya"

    Jikinta gaba daya rawa yakeyi"

   Abba ko ido ya kureta dashi zuwa can yace, yau naje gidan malam idris na tuntubeshi game dake, ya nunamin komai lfy kuma kina karatu sosai yadda ya kamata, amman abinda ya bani mama cewa da yayi wai baki zuwa makaranta akan lokaci, bayan nikuma nasan kina fita gida da wuri"

    Shiru Abba yayi yana jiran yaji me zata ce"

    Jita shiru yasa yace badake nake mgn ba"

   Kanta akasa tace Abba wlh ni babu inda nake zuwa"

   Amman kinsan malam idris bazaimin karya ba ko?

     Nasani abba, amman ni daga nafita wlh tallahi banazuwa ko ina sai makaranta, sai dai idan kafin naje lokaci yake kure ....

    Cikin ido abba ya kalleta sannan yace bari rantsuwa, ai bacewa nayi ki rantse ba, bakomai daga yau drive zai dinga kaiki makaranta, idan lokacin tashi yayi zai dawa ya daukeki, haka yayi ko ?

    Daga kai tayi badan ranta yaso ba"

  Juyawa abba yayi ya kalli usman sannan yace kaikuma me kazoyi da daddaren nan ?

    Cikin natsuwa ya fara fada mishi komai kamar yadda mama tafada mai, sannan ya kara da cewa abba ya kamata adauki mataki akanta be kamata azuba mata ido tanayin abinda taga dama ba"

   Shiru falon yayi zuwa can abba ya nisa sannan yace...

    Ke !! Asma'u wani abu na damun ki ne?

  Cikin sauri ta girgiza kai tare da fadin a'a"

   Akwai wani abunda kikeson ne ko kike son a saya miki ?

  Nan ma a,a ta sake cewa"

   Shiru abba yayi sannan yace....

  Ninasan abinda ke damun ki, Aure ne baki so, kuma bazai yiyoba, tun ranan dana miki mgnr aure kika fara koke2  ita kuma dada ta biye miki har tana taya Ki, bazan kara kaiki gidan ba bare ki kara sata  kuka"

    Juyawa yayi ya kalli mama sannan yace wlh tun ranan danakaita gidan, dada na nan babu lfy, yanzun jiya nakaita asibiti sunce jininta ya fara hawa"

     Juyawa yayi ya kara kallon asma,u sannan yace ki shirya gobe zakiyi bako, ni ba nufina namiki auren dule ba, a'a zaizo ne ya ganki, kema ki ganshi, idan kun daidaita shikenan, idan kuma baku daidaita ba zan sake turo wani, bana bukatar kice wai saikinsa halinshi, duk wandan
 kikaga na turo miki na yadda da inganshi tare da mutuncin iyayen sa, dan haka kwana 2 kawai na baku, ganin inda tayi shiru yasa abba fadin kinajina ko ?

 
   Kai kawai ta iya dagawa sannan tasa hannunta ta share hawaye"

   Tattaunawa suka fara tsakanin mama da abba tare da yaya usman, haka ne yabata daman tashi tabar musu falon"


        ****


 Washegari ma'u ta tashi da matsanan cin ciwon kai, saka makon rashin baccin da batasamu, taso taki zuwa mkrnt amman kuma tanason taga halin da ummi take ciki, dan haka ta mike tahau shiri"

    Drive ne ya kaita har bakin mkrntr sannan ya juya, dan kaka bata samu daman zuwa gidan su deeni ba saida aka tashi break"

   Xama sukayi jugum ita da ummi kamar masu zaman makoki"

 Bayan antashi makaranta abba da kanshi yazo ya dauketa"

  Koda ta shiga gida a kitchen ta samu mama tanata soye2 sai alokacin ta tona da bakon da abba yace zaizo"

   Yatsuna baki tayi sannan ta juya ta shige daki, wanka tayi tai sallah sannan ta tsaya tai addu'a sosai Allah ya kubutar da deeni daga hannun Jamal"

   Tana zaune kan sallayan mama tashigo tana fadin Asma'u maza ki fito bakonki ya iso"

    Gabanta taji ya fadi, kanta ta daga ta kalli mama sannan tace...
   Mama dan Allah kice bacci nake, nifa  bansan mezance mai ba"

   Shiru mamatayi zuwa can tace, kinga, Asma'u banason shirme maza ki fito ko na kira abbanki na gayamai"

    Cikin sauri ta mike tana matso hawaye ta nufi hanyan kofa"

    Ke !! Zonan mama ta fada tana kare mata kallo"

   Bayan ta juyo tace nufinki ahaka zaki tafi fuska saikace tsowar me takaba"

   Bakinta agaba tace to ai yanzun nan fah nayi wanka"

    Mama batace komai ba ta juya ta fara ciro mata kaya, mika mata tayi ta Saka sannan ta zaunar da ita dakanta ta mata kwalliya bawata me hayaniya ba"

    Madaidaicin gyale ta mika mata dasukai matukar dacewa da kayan datasa, kallo ta kare mata sannan tace toh maza ga kayan motsa baki can na hada ki dauka ki tafi dashi"

   Jikinta babu kwari ta nufa kitchen tare da nazarin abinda zata ma bakon ta kuntuka mishi haushi"

   Ahankali ta tura kofar falon abba tare da sallama cikin siririyar muryanta, cikin ido ta kalli bakon nata farine babu laifi yana da kyau daidai misali, saidai daganin shi yana da iyali, duk da cewa bawani babba bane amman daganin shi yana da iyali, sauke idonta tayi akanshi sannan ta karasa shiga falon tare da neman yadda zata mishi"

    Kayan motsa bakin ta ajeye agefen shi sannan ta koma tsakiyan falon ta tsuna, cikin ladabi tace...

     Inakwana daddy, ina gajiya, bata jira ya amsa ba taci gaba da cewa gashi kazo kuma abban bayanan ya tafi Office amman idan ya dawo zan fadamishi kazo"

   Cikin mamaki yake kallonta aranshi yace lallai wannan yariya da hikima take, idan na fahimceta tana nufin namata tsufa, gyaran murya yayi sannan yayi murmushi yace, toh shikenan asma'u idan ya dawo din ki gaya mishi, amman wa zaki ce masa?

     Rasa abun cewa tayi zuwa can tace zance masa bayan fitanshi wani yazo neman shi"

   Murmushi ya sake zaiso kasancewa da wannan yariyar,  kallonta yayi ya girgiza kai sannan yace kinada abin dariya, ni sunana Jafar inada mata 1 da yara na guda 2 nine bakon da mahaifi ki ya sanar dake zuwan Sa, duk da nasan kinsan koni waye"

    Ko kallon gafen shi batayi ba acikin zuciyarta tace wato abba neman kai yake dani, ya rasa wadda zai turomin sai me mata, dumi taji akumatun ta tana shafowa taji hawaye"

    Duk abin da take bakonta na kallonta dan haka ya mike yace nizan tafi sai ince ki gaida mutanen gida"

    Bata ce komai ba yasa hannu ya ciro kudi aljihu ya aje agefen kujera yayi waje dan yaga bata da niyar kula shi"

    Itama ficewa tayi batare da ta dau kudin da ya ajiye mata ba, bare kayan motsa bakin datakai mai"

    Afalo ta wuce mama ta shige dakinta, zama tayi tare da addu'a Allah yasa abban ya janye wannan kudirin  nashi"

     Washegari da safe ta shirya tsaf domin zuwa mkrnt falon abba ta fara shiga, bayan ta gaisheshi ta mike zata wuce abba ya dakatar da ita"

    Komawa tayi ta zau tare da sauke kanta akasa"

   Kallonta abba yayi sosai sannan yace bakon ki yazo jiya ko?

   Kanta akasa tace eh"

    Shiru ne ya ziyarci falon zuwa can abba ya sake cewa...
   To me kika ce ? Ya miki ?

    Shiru tayi bata ce komai ba, zuwa can abba ya sake cewa....

  Karmuyi haka dake mamana, banason na takuraki saboda kin min biyayya saboda haka nakeson na saka miki, wadda kike so shi zan baki bazan miki auren dole ba da iznin Allah, inason nasan meye azuciyar ki game da jafar ?

     Motsa baki tai tayi daker ta iya bude baki tace Abba ni banason shi"

    Saboda me ? abba ya tambaya

    Abba tsoho ne fah kuma yana da mata"

    Murmushi Abba yayi kadan sannan yace ashe jafar ya cinka daidai, toh bakomai amman nayi miki sha,wan shi, dan yaro ne me mutunci da sanin ya kamata, haka iyayen shi mutane ne masu karamci, kuma bawani babba bane mamana, ko zai girmin usman bazai wuce shekara daya ba, amman ba komai tunda kince haka, gabe wani zaizo ki ganshi, kinji ko?

   Saida gabanta ya fadi wato abba bazai bar mgn haka ba, da wannan tunanin ta tafi mkrnt ko wa Abba zai sake turo mata oho?

       ***

  Akofar gidan su deeni ta hango samari cike, da alama yaran duna ne kome suke agurin oho, acikin su caka kawai ta sheda yanata fada yana daga hannu saidai har motan su ta wuce bata tsinci abinda suke cewa ba"

    Ko a aji batai karatun kirki ba Allah2 take atashi break taje taga me akeyi"

   Kawayen ta kallonta kawai sukeyi, domin sun kula akwai abun da ke damunta"

   Ana buga kararrawa ta fito ta nufi gidan su deeni saidai yazun babu kowa akofar gidan"

    Cikin gidan ta nufa tana tura kofar sukayi ido 4 da deeni, zaune yake kan kujera ummi tsugune agefen shi tana tsuma tsunma aruwa zafi tana dannan me ajikin shi"

    Hunnu tasa ta mumtsuke idonta sannan ta sake sauke shi akan deeni, aguje tayi kansu, jinta kawai tayi jikin deeni ya rungume ta yana sumbatan ta"

   Cikin sauri ummi ta dauke bokitin ruwan zafinta ta basu guri, jefe2 tana satan kallon su"

    Sun dan juma ahaka ahankali asma'u ta zame ta koma gefe sannan ta zubawa deeni ido"

     Shedan bulala ne ajikin shi rudu2 wasu guraren hadda ciwo, hawaye taji ya cika mata ido, nan danan suka fara zubowa acikin kuka tace nina jawo maka nasan bakowa bane yayi maka haka sai Jamal dan Allah ka yafe min"

   Hannuta ya jawo ya riketa dakyau sannan yace....

    Shine Asma'u amman karki damu yanaso ne wai ya nunamin shi Soja ne amman ba jarumi ba, wanna abin daya aikata ya nunamin be kai ba"

    Kara karkace baki yayi sama sannan yace.....
Ai nagaya masa dan *uwas* data haife shi, idan yana jin yakai shege, ya goyo *uwassa* abaya, ya fadi ina zamu hadu, daban daban zasu koma gida"












   Heart beat
*Mmn Yazeed*






Yayan ki *Jamal*

Mikewa ma'u tayi da sauri sannan tayi jifa da ledan " bantawa tayi tacire wayar acikin kwali dan haka ta dauki kwalin ta buga da kasa" sai lokacin ta kula dan haka ta dauki wayar ta makawa bango"

   Ji kake tassss"

   Da gudu ta fita ta nufi dakinta ta fada gado tare da saka sabon kuka"


    Wato Jamal ne yaje har gida ya kama deeni ? Ko tantama batayi Jamal ne wani sabon tsanan shi taji axuciyarta ji take kamar ta kashe shi"

     Tashi tayi ta zauna yanzun meye abinyi ?

   Yaya zanyi inkubutar da deeni daga hannun Jamal


Mama ko mamakin hali irin na ma'u tayi sannan ta juya ta kalli bannan da tayi ta girgiza kai, cike da takaici ta fita adakin"

   Da misalin karfe biyu da rabi ma'u ta fito cikin shirin tafiya mkrnt yamma, kallonta mama tayi taga idonta duk sun kumbura cikin idonta jawur sun kankance, da alamar ma ko cire kayan makaratar batayi ba tunsafe, dauke idol tayi akanta domin al'amarinta ya fara bawa mama haushi"

   Saida ta turu baki tace natafi"

  Ko kallonta mama batayi ba tace adawo lfy"

     Kaitsaye gidan su deeni ta shiga, ummi nazaune ta tasa abinci agaba ta kasa ci"

    Gabata ma'u ta zauna ta bude sabon kuka, hankalin ummi kara tashi yayi, rufe abincin tayi sannan tace ki daina kuka Asma'u bakiga inda fuskan ki ta kunbure ba, mutaru miyi hakuri inada tabbacin auta na zai dawo gida domin nasan shiba rago bane, wannan tashin hakalin da kika ganni ci narashin tabbacin inda yake ne da rashin sanin halin dayake ciki amman da yardan Allah auta zai dawo"

    Dahaka ummi ta samu ta shawo kan ma'u, ta wuce makaranta"

    Da daddare Asma'u na kwance afalo tana cigaba da tunanin deeni badan tana tunanin kar asirinta ya tonu ba data ansa no Jamal agun yaya usman ta bashi hakuri ya sakar mata deeni"

    Tana cikin wannan tunanin taji sallaman yaya usman rufe ido tayi kaman me bacci, Allah2 take ya wuce amman saitaji ya zauna akujeran dake kallon nata"

   Zuwacan mama ta fito tana fadin ka iso?

   Eh naje gidan momy yanzun tacemin kina nema"

   Zama tayi sannan tace eh Daman Asma'u ce gatanan narasa gane mata, kwashe duk yadda akayi tayi ta gaya masa"

     Sannan ta nuna masa yadda tayiwa wayar da Jamal ya kawo mata"

   Cike da baccin rai yace mama bawani abinda yake damunta banda iskanci da sangarta, bataga ba,a dukanta ba kuma ai ba wuce dukan tayi ba, dan ubanta Jamal din sa'anta ne

     Usman na tsaka da fada Abba ya shigo, daga mama har usman sannu suke mai" amman abban yaki amsawa fadin yake ina Asma'u

   Toh fah mama ta fada azuciyarta domin indai taji alhaji ya kira ma'u da sunan ta toh akwai mgn"

    Itako ma,u tanaji Abba ya kira sunanta ta bude ido tare da sakkowa akan kujeran azuciyarta tace shikenan dada ta fadawa abba"

    Kusa da ita abba ya zauna sannan ya rike hannunta guda daya"

    Jikinta gaba daya rawa yakeyi"

   Abba ko ido ya kureta dashi zuwa can yace, yau naje gidan malam idris na tuntubeshi game dake, ya nunamin komai lfy kuma kina karatu sosai yadda ya kamata, amman abinda ya bani mama cewa da yayi wai baki zuwa makaranta akan lokaci, bayan nikuma nasan kina fita gida da wuri"

    Shiru Abba yayi yana jiran yaji me zata ce"

    Jita shiru yasa yace badake nake mgn ba"

   Kanta akasa tace Abba wlh ni babu inda nake zuwa"

   Amman kinsan malam idris bazaimin karya ba ko?

     Nasani abba, amman ni daga nafita wlh tallahi banazuwa ko ina sai makaranta, sai dai idan kafin naje lokaci yake kure ....

    Cikin ido abba ya kalleta sannan yace bari rantsuwa, ai bacewa nayi ki rantse ba, bakomai daga yau drive zai dinga kaiki makaranta, idan lokacin tashi yayi zai dawa ya daukeki, haka yayi ko ?

    Daga kai tayi badan ranta yaso ba"

  Juyawa abba yayi ya kalli usman sannan yace kaikuma me kazoyi da daddaren nan ?

    Cikin natsuwa ya fara fada mishi komai kamar yadda mama tafada mai, sannan ya kara da cewa abba ya kamata adauki mataki akanta be kamata azuba mata ido tanayin abinda taga dama ba"

   Shiru falon yayi zuwa can abba ya nisa sannan yace...

    Ke !! Asma'u wani abu na damun ki ne?

  Cikin sauri ta girgiza kai tare da fadin a'a"

   Akwai wani abunda kikeson ne ko kike son a saya miki ?

  Nan ma a,a ta sake cewa"

   Shiru abba yayi sannan yace....

  Ninasan abinda ke damun ki, Aure ne baki so, kuma bazai yiyoba, tun ranan dana miki mgnr aure kika fara koke2  ita kuma dada ta biye miki har tana taya Ki, bazan kara kaiki gidan ba bare ki kara sata  kuka"

    Juyawa yayi ya kalli mama sannan yace wlh tun ranan danakaita gidan, dada na nan babu lfy, yanzun jiya nakaita asibiti sunce jininta ya fara hawa"

     Juyawa yayi ya kara kallon asma,u sannan yace ki shirya gobe zakiyi bako, ni ba nufina namiki auren dule ba, a'a zaizo ne ya ganki, kema ki ganshi, idan kun daidaita shikenan, idan kuma baku daidaita ba zan sake turo wani, bana bukatar kice wai saikinsa halinshi, duk wandan
 kikaga na turo miki na yadda da inganshi tare da mutuncin iyayen sa, dan haka kwana 2 kawai na baku, ganin inda tayi shiru yasa abba fadin kinajina ko ?

 
   Kai kawai ta iya dagawa sannan tasa hannunta ta share hawaye"

   Tattaunawa suka fara tsakanin mama da abba tare da yaya usman, haka ne yabata daman tashi tabar musu falon"


        ****


 Washegari ma'u ta tashi da matsanan cin ciwon kai, saka makon rashin baccin da batasamu, taso taki zuwa mkrnt amman kuma tanason taga halin da ummi take ciki, dan haka ta mike tahau shiri"

    Drive ne ya kaita har bakin mkrntr sannan ya juya, dan kaka bata samu daman zuwa gidan su deeni ba saida aka tashi break"

   Xama sukayi jugum ita da ummi kamar masu zaman makoki"

 Bayan antashi makaranta abba da kanshi yazo ya dauketa"

  Koda ta shiga gida a kitchen ta samu mama tanata soye2 sai alokacin ta tona da bakon da abba yace zaizo"

   Yatsuna baki tayi sannan ta juya ta shige daki, wanka tayi tai sallah sannan ta tsaya tai addu'a sosai Allah ya kubutar da deeni daga hannun Jamal"

   Tana zaune kan sallayan mama tashigo tana fadin Asma'u maza ki fito bakonki ya iso"

    Gabanta taji ya fadi, kanta ta daga ta kalli mama sannan tace...
   Mama dan Allah kice bacci nake, nifa  bansan mezance mai ba"

   Shiru mamatayi zuwa can tace, kinga, Asma'u banason shirme maza ki fito ko na kira abbanki na gayamai"

    Cikin sauri ta mike tana matso hawaye ta nufi hanyan kofa"

    Ke !! Zonan mama ta fada tana kare mata kallo"

   Bayan ta juyo tace nufinki ahaka zaki tafi fuska saikace tsowar me takaba"

   Bakinta agaba tace to ai yanzun nan fah nayi wanka"

    Mama batace komai ba ta juya ta fara ciro mata kaya, mika mata tayi ta Saka sannan ta zaunar da ita dakanta ta mata kwalliya bawata me hayaniya ba"

    Madaidaicin gyale ta mika mata dasukai matukar dacewa da kayan datasa, kallo ta kare mata sannan tace toh maza ga kayan motsa baki can na hada ki dauka ki tafi dashi"

   Jikinta babu kwari ta nufa kitchen tare da nazarin abinda zata ma bakon ta kuntuka mishi haushi"

   Ahankali ta tura kofar falon abba tare da sallama cikin siririyar muryanta, cikin ido ta kalli bakon nata farine babu laifi yana da kyau daidai misali, saidai daganin shi yana da iyali, duk da cewa bawani babba bane amman daganin shi yana da iyali, sauke idonta tayi akanshi sannan ta karasa shiga falon tare da neman yadda zata mishi"

    Kayan motsa bakin ta ajeye agefen shi sannan ta koma tsakiyan falon ta tsuna, cikin ladabi tace...

     Inakwana daddy, ina gajiya, bata jira ya amsa ba taci gaba da cewa gashi kazo kuma abban bayanan ya tafi Office amman idan ya dawo zan fadamishi kazo"

   Cikin mamaki yake kallonta aranshi yace lallai wannan yariya da hikima take, idan na fahimceta tana nufin namata tsufa, gyaran murya yayi sannan yayi murmushi yace, toh shikenan asma'u idan ya dawo din ki gaya mishi, amman wa zaki ce masa?

     Rasa abun cewa tayi zuwa can tace zance masa bayan fitanshi wani yazo neman shi"

   Murmushi ya sake zaiso kasancewa da wannan yariyar,  kallonta yayi ya girgiza kai sannan yace kinada abin dariya, ni sunana Jafar inada mata 1 da yara na guda 2 nine bakon da mahaifi ki ya sanar dake zuwan Sa, duk da nasan kinsan koni waye"

    Ko kallon gafen shi batayi ba acikin zuciyarta tace wato abba neman kai yake dani, ya rasa wadda zai turomin sai me mata, dumi taji akumatun ta tana shafowa taji hawaye"

    Duk abin da take bakonta na kallonta dan haka ya mike yace nizan tafi sai ince ki gaida mutanen gida"

    Bata ce komai ba yasa hannu ya ciro kudi aljihu ya aje agefen kujera yayi waje dan yaga bata da niyar kula shi"

    Itama ficewa tayi batare da ta dau kudin da ya ajiye mata ba, bare kayan motsa bakin datakai mai"

    Afalo ta wuce mama ta shige dakinta, zama tayi tare da addu'a Allah yasa abban ya janye wannan kudirin  nashi"

     Washegari da safe ta shirya tsaf domin zuwa mkrnt falon abba ta fara shiga, bayan ta gaisheshi ta mike zata wuce abba ya dakatar da ita"

    Komawa tayi ta zau tare da sauke kanta akasa"

   Kallonta abba yayi sosai sannan yace bakon ki yazo jiya ko?

   Kanta akasa tace eh"

    Shiru ne ya ziyarci falon zuwa can abba ya sake cewa...
   To me kika ce ? Ya miki ?

    Shiru tayi bata ce komai ba, zuwa can abba ya sake cewa....

  Karmuyi haka dake mamana, banason na takuraki saboda kin min biyayya saboda haka nakeson na saka miki, wadda kike so shi zan baki bazan miki auren dole ba da iznin Allah, inason nasan meye azuciyar ki game da jafar ?

     Motsa baki tai tayi daker ta iya bude baki tace Abba ni banason shi"

    Saboda me ? abba ya tambaya

    Abba tsoho ne fah kuma yana da mata"

    Murmushi Abba yayi kadan sannan yace ashe jafar ya cinka daidai, toh bakomai amman nayi miki sha,wan shi, dan yaro ne me mutunci da sanin ya kamata, haka iyayen shi mutane ne masu karamci, kuma bawani babba bane mamana, ko zai girmin usman bazai wuce shekara daya ba, amman ba komai tunda kince haka, gabe wani zaizo ki ganshi, kinji ko?

   Saida gabanta ya fadi wato abba bazai bar mgn haka ba, da wannan tunanin ta tafi mkrnt ko wa Abba zai sake turo mata oho?

       ***

  Akofar gidan su deeni ta hango samari cike, da alama yaran duna ne kome suke agurin oho, acikin su caka kawai ta sheda yanata fada yana daga hannu saidai har motan su ta wuce bata tsinci abinda suke cewa ba"

    Ko a aji batai karatun kirki ba Allah2 take atashi break taje taga me akeyi"

   Kawayen ta kallonta kawai sukeyi, domin sun kula akwai abun da ke damunta"

   Ana buga kararrawa ta fito ta nufi gidan su deeni saidai yazun babu kowa akofar gidan"

    Cikin gidan ta nufa tana tura kofar sukayi ido 4 da deeni, zaune yake kan kujera ummi tsugune agefen shi tana tsuma tsunma aruwa zafi tana dannan me ajikin shi"

    Hunnu tasa ta mumtsuke idonta sannan ta sake sauke shi akan deeni, aguje tayi kansu, jinta kawai tayi jikin deeni ya rungume ta yana sumbatan ta"

   Cikin sauri ummi ta dauke bokitin ruwan zafinta ta basu guri, jefe2 tana satan kallon su"

    Sun dan juma ahaka ahankali asma'u ta zame ta koma gefe sannan ta zubawa deeni ido"

     Shedan bulala ne ajikin shi rudu2 wasu guraren hadda ciwo, hawaye taji ya cika mata ido, nan danan suka fara zubowa acikin kuka tace nina jawo maka nasan bakowa bane yayi maka haka sai Jamal dan Allah ka yafe min"

   Hannuta ya jawo ya riketa dakyau sannan yace....

    Shine Asma'u amman karki damu yanaso ne wai ya nunamin shi Soja ne amman ba jarumi ba, wanna abin daya aikata ya nunamin be kai ba"

    Kara karkace baki yayi sama sannan yace.....
Ai nagaya masa dan *uwas* data haife shi, idan yana jin yakai shege, ya goyo *uwassa* abaya, ya fadi ina zamu hadu, daban daban zasu koma gida"












   Heart beat
*Mmn Yazeed*

​[12/10, 8:15 PM] ‪+234 810 828 9060‬: 💗💝💝💗
​*BUGUN ZUCIYA*​
   ( ​Heartbeat​)

                   💓💝💗
                        💗           

💓💝💗
​By​
     💗
    ​​*Fadeela Lamido*




*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*


   

Dedicated 👇🏻
*Sa'adatu Lamido👌🏻*



      3⃣1⃣ to 3⃣2⃣





🙉🙉 Hannu shi yasa yana share mata hawaye, yana cigaba da fadin.....
   Ki daina zubar da hawayen Ki abanza ni be tsoratani ba kuma banyi nadamar hadashi da duna ba, kisan menene, tuhumata yakeyi akan ki"

   Ido ta zare akaina kuma?

    Eh dan ya nemi nabashi takardan da kika wurgu min da ita"

    Tashin hankali bai yane afuskan ta tace... Kabashi ne?

    A'a na nunamai bansan wannan zancen ba, amman sai naga yayi dariya, na lura kanshi na aiki sosai, murmushi deeni yayi kadan sannan yace.....
   Asma'u da kika samu lbrn Sojoji sun tafi dani ya kikaji?

  Wani sabo hawaye ne ya fara zobo mata cikin kuka tace....
   Komawa nayi tamkar marainiya, kullum cikin kuka nake, gashi ranan na taho da matsalata, domin mune mi mafuta, wlh ranan jinayi kaman bani da lfy, kuma bansan abinda kemin ciwo ba, tun daga ranan hankali na bekara kwanciya ba, kum.....

   Deeni ne ya matse hannun ta, dan haka ta kasa karasa abin da tayi niyya, sannan ta daga ido ta kalleshi"

     Shima ita yake kallo sannan yace.....
    Inason nasan wacce matsala ce kikazo da ita ranan?


     Shiru tayi zuwa can tace abbana ne yace.....
  Inayin sauka zai min aure, kuma gashi saura sati 6, yace bazan wuce wata 3 agida ba, shine hankali na ya tashi sosai"

     Hannunta ya kara runtsewa sannan yace.....

    Toh menene abin damuwa anan Asma'u ?, ko bakison muyi aure ne ?

     Shiru tayi tana kallon kasa, zuwacan taji ya sake cewa....

   Gayamin meye matsalan ?

    Kanta akasa tace inajin tsoron gayawa abbana kai nake so"

    Matse hannunta yayi da karfi harsai da tayi kara, cikin yanayi irin na mejin zafi tace.....
   Wayyo, hannuna dan Allah kabari da
Zafi fah"

   Me yasa kike tsoro? taji ya fadi fuskan shi murtuk"

    Saboda ina tunanin bazai yadda ba"

    Bangane bazai yadda ba, shi zai zauna miki da miji ?

    A'a ba haka bane, ta fada tare da kautar da idanta gefe, haka nan taji bata ji dadin furucin ba, sai take ga kamar da raini aciki"

     Shiko ido ya kura mata zuwa can yace.... Inajin ki"

   Idan ta kwal2 yayi kaman zatai kuka tace....
   Yaya deeni ni. nasan waye abba na, mawuyacin abu ne ya amince dakai, ko hankan zata kasan ce ko, to saida sa hannun kakata, kuma nafara mata zancen duk tabi ta firgice, saboda ta tsorata dakai, gashi abbana jiya ya turo min wani mutumi wai mu daidaita, karashe mgnr tayi tana zubar da hawaye"

    Tana rufe baki deeni ya zabura ya mike tsaye, kashi ya daga sama yana kallon sararin samaniya tare da fadin..... Kikace baban ki ya turo miki wani ?

    Kaita daga alamar eh"

 Kuma wadda aka turo din yaxo ?

    Eh tasake cewa tanabin kanshi daya dage sama da kallo"

    Shiru yayi, zuwa can yace..... Kinyi mai dariya ne?

    A'a"

   Mgn fah ?

   Ahankali ta shiga fada mishi yadda sukayi da jafar"

    Ajiyan zuciya ya sauke sannan ya sakko da kan shi ya kalleta, hannushi Yasa ya dagota sannan ya saki murmushi tare da fadin, na yadda kina sona, kuma duk wadda ya sake turo miki karki yadda ki kulashi bare har kimai dariya, ke bama haka ba, ko fuskanki karki yadda wani ya gani"

   Shiru yayi ya kura mata ido sannan yace kince babanki  dan rayi ne ko?

    Shiru tayi ta kasa bashi amsa, dan tasan darajan abban ta, tsoro take kar yazo ya fadin mata wata mummunan kalma akan abbanta"

    Shiru yaji dan haka deeni ya sake cewa.... Kakar nan taki mamanki ta haifa ko babanki ?

   Jimmm ma'u tayi sannan tace abbana"

   A haf, a gurita ya dauko, dan kakar nan taki, lutiyar munafuka ce, amman bakomai Wata rana zamu hadu"

   Mamaki furucin deeni bawa ma'u, nan take ta fara hawaye wannan ai zagi ne, yana nufin abbanta ma munafuki ne kenan, cikin matsanan cin kuka ta mike tare da kwace hannunta daga rukon daya mata"

    kofar gidan ta nufa, cikin sauri ya mike yabi bayanta , tana daf da fita ya riketa, ganin inda take hawaye yasashi fadin menene ?, na miki wani abune ?

    Wani sabon haushi ne ya sake kamata dan haka kukanta yaki tsayawa"

     Ganin inda take kuka ya sashi ya kwalawa ummi kira"

   Bayan ta iso yace ummi kinga yariyar nan munacikin mgn ta rikece min da kuka"

   Hannuta ummi ta rike suka shiga daki, deeni yaso shiga Amman ummi tace yajira su awaje"

   Zuwa can suka fito ummi rike da hannun ma'u tana kara rarrashinta tare da share mata hawaye"

   Ummi me tace miki? Deeni ne ya tambaya tare da tsare su da ido"

   Auta ina yawan gaya maka karinka gyara kalamin ka, iyaye fah ba,abin wasa bane"

   Nan take ya fahimci laifin shi dan haka bejira ummi ta gama mgn ba yaja hannu ma'u yayo waje da ita"

     Akofar gida yaja ya tsaya sannan ya kalleta yace..... Allah ya huci zuciyar ki, basan mgnr zata baki haushi ba, lallai kinason abban nan naki, gashi shi kuma ko kadan be damu dake ba, ganin inda ta daure fuska yasashi ya kama kunnen shi duk 2 sannan yace na tuba"

     Be barta ta tafi ba harsai da yaga ta saki jikinta, tana dariya"

       ****


Washegari da misalin karfe 5:00pm bakon Asma,u na 2 ya iso"

    Tafiya take jiki babu kwari domin isa falon da abba ya ke sauke baki, zuciyarta cike da tunanin deeni dan komai takeyi jitake kamar ana kara mata sonshi"

     Tana shiga falon da kujeran data fara cin karo ta zauna sannan ta juya mai baya"

    Bata ce kala ba shima bece komai ba, sun kwashi kusan minti 15 ahaka, sannan taji wata siririyar murya tace..... hajiya ba mgn ne?

    Yi tayi kamar bata jishi ba, dan haka ya miki ya dawo kujeran dake kallon tata, cikin sauri ta sake juyawa ta kalli ban garen daya baro, kafarta daya ta daura akan daya tana dan girgizawa"

   Jitayi yana fadin OK nine bazaki kalla ba kenan, toh idan ke bazaki kalleni ba ni kibari nagan ki"

     Nan ma shiru yaji kada kafa kawai take"

    Zuwa can ya sake cewa Asma'u ni akan hanya nake, ya kamata ki juyo muyi mgn yamma nayi"

    Batace kala ba dan haka ya mike yana fadin OK shikenan, na fahimta, bekara cewa komai ba yayi waje"

    Koda ta shiga gida bata tayar da hankalin taba harkokin ta ta shiga yi, dan idan ta tuna abba yace bazai mata auren dole ba hankalinta na kwanciya"

   Washegari da safe abba ya aiko kiranta, hijabi ta dauka dogo har kasa ta saka sannan ta nufi falon abba"

    Tun abakin kofar taji wata murya kaman ta *Jamal* suna gaisawa da abba"
 
    Gabanta taji ya fadi tare da tunani yaushe yashigo gidan nan da sanyi safiyar nan yazu musu gida?

    Tana shiga suka hada ido da *Jamal* yana zaune cikin kakin sa, agaban abba ya zauna ya cire hular shi, tare da tankwashe kafa, kamar wani me daukan karatu"

    Yana ganinta ya dauke idon shi, tsunawa tayi ta gaida Abba sannan ta juya ta gaida Jamal"

    Ciki2 ya amsa, kamar wanda be iya mgn"

     Abba ko daure fuska yayi sannan ya dawo da hankali shi gareta, acikin bacin rai yace.....
   Mamana kin fara bata min rai fah, ya zan turo miki bako kimai shiru?, towai tukuna ma, me kike nufi ne ?, nakula lamarin ki akwai abin dubawa aciki, toh bari nagaya miki niba mutumin banza bane, bazan dauki iskanci ba, duk yadda akayi acikin 2 za,a samu daya kodai wani ke hure miki kunne, ko kuma kinason kita zama agida har ki tsofe, amman banda iskanci ya zan turo miki bako ki banza dashi??

     Asma'u kuka kawai take harda shashsheka, zuwa can taji muryan Jamal yana cewa....
     Abba tunda bata so abarta mana, ai naga bawani girma tayi ba"

    Au, au haka zakace, eh dole kace haka tunda kaima auren ba damun ka yayi ba, Abba ya fada sannan ya koma kan ma'u yace zan turo miki bako na karshe acikinsu, su 3 nan dole ki dauki daya, idan kuma kinada wani boyayye ne wadda kike so to kidaina wahalar dani"

      Kuka ma'u tai tayi agaban Abba zuwa can taga ya juya gurin Jamal sun cigaba da hira, mikewa tayi tana kokarin fita taji Jamal nawa Abba sallama"

   Da sarauri yake tafiya dan haka yacin mata, angajeta yayi kadan sannan ya juya ya kalleta yace..... toh ballagaza saboda rashin hankali kina kallo na kuma kika bege ni"

    Cikin murya irinta wadda yaci kuka ya koshi tace ai kaine ka begeni bani ba"

    Hannu ya mika ya murde mata kunne, batasan sannan da ta kwallah kara ba"

    Mama ce tafito da sauri tana fadin menene ya faru?

   Tseye ta same su ganin mama yasa shi ya saki kunnen, yana fadin mama wlh yariyar nan bata da kunya, tana ganina fa amman saita ture ni"

   Juyawa mama tayi tana fadin wlh kabata kashi, batabari mama ta wuce ba tabi bayanta da gudu tana mamakin halin Jamal, wato banda mugunta kuma harda sharri?

   Tundaga ranan abba be sake mata zancen aure ba, har ranan saukan su tazo, anyi sauka nagani na fada, abba yayi farin ciki sosai ganin inda ma'u take raira karatu hawaye yaji yana zubo mishi saboda tsabar farin ciki, addu'a ya fara Allah ya nuna mishi ranan aureta haka, itama ma,u farin ciki tayi sosai ganin dangi duk sun hallara kuma duk dominta"

    Deeni ne kawai babu agurin tayi2 yasa manyan kaya yazo, amman yace shi bazai saka ba dan tunda yake betaba saka manyan kaya ba, dan haka tayi fushi tace karyazo"

    Sun yi sauka da kwana 2 Abba ya aiko kiranta, mgnr dai daya ce gobe bakonta zaizo"

   Kin tashi tayi tai zaune ta fara kuka, banza abba yayi da ita ya juya yaci gaba da rubuce2"

    Suna haka alhaji musa ya shigo, ganin ta haka yasashi tambayan lfy?

   Abba ne ya gayamai duk halin da ake ciki, shiru yayi zuwa can ya juya ya kallai ta yace"
   Asma'u duba, ai shi aure dole ne, dan haka idan Allah yaso, nan da sati 2 kina dakin mijin ki, ko akwai wadda kike so ne?

   Motsa baki ta fara amman ta kasa bude baki"

   Alhaji musa ya sake cewa inajin ki, nakula bakin ki akwai mgn

   Dago kata tayi ta kale abba sanna ta sake maida kanta kasa hawaye na zubowa tare da majina"

   Abba ne yace ni Ki daina kallo na, ki fadi abin da ke bakin Ki"

    Alhaji musa cikin tohoma yake kallon ta sannan yace....
   Kina da wadda kike so ne?

    Ahankali ta daga kai, saika kula sosai zaka gane"

   Abba tashi yayi ya zauna sosai sannan yace waye shi?

   Alhaji musa ne yayi murmushi sannan ya a,a bahaka za'ayi ba, ta turo mana shi kawai, ai daman mu bamu da burin yi miki auren dole, dan haka ki gaya masa munason ganin shi"

    Ciki2 tace abba iyayen shi ne zasu zo, ko shi?

    Girgiza kai Abba yayi cikin takaici, alhaji musa ne yace shi dai muke son gani kafin ajega mgnr iyayen sa, ai kisan aure yana son bincike ko ?













Heart Beat
*Mmn Yazeed*​
[12/10, 8:16 PM] ‪+234 810 828 9060‬: 💗💝💝💗
​*BUGUN ZUCIYA*​
   ( ​Heartbeat​)

                   💓💝💗
                        💗           

💓💝💗
​By​
     💗
    ​​*Fadeela Lamido*




*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*



Dedicated 👇🏻
*Firdausi Sodangi Aisha Aliyu Garkuwa & Deeje Waziri*😍😍



        3⃣3⃣to3⃣5⃣



🖤 Tashin hankali ma'u ta shiga tunkafi tabar falon, mikewa tayi jiki babu kwari ta koma dakin ta"


   Ko acan din ma tunani ta shigayi, ta yaya zata kawo deeni gidan su, anya idan abba yaga deeni bazata fuskanci tashin hankali ba kuwa?

    Hakika da ace zan iya hakura da deeni, da komai yazo min da sauke saidai bazan iya ba, yanzun ne ma nakejin son shi acikin zuciyata"

   Shiru tayi tana tunanin hanyar da zatabi su hadu da deeni ayau"

    Tana cikin wannan tunanin taga abba ya turo kofa, idonshi jawur har sun dan tasa"

    Bakin gadon yazo ya zauna, yayi jugun yana kallan kasa"

   Tsoro ne ya kama ma'u, kodai abba dokana yazo yi, wannan tunanin yasa ta fara ja da baya harta sauka agadon ta tsuna akasa"

   Kallonta abba ya sake yi, sannan ya maida idon shi kasa, yayi haka kusan su uku sannan ya mike tsaye ya goya hannushi abaya, cikin wata irin murya wadda batasan Abba na da itaba taji yace.... Asma'u kin munafunce ni, tuntuni naso na miki aure amman sai kika nunamin ke ba yanzun ba, sai ayanzun naga laifina dana biye miki, shiru yayi zuwa can yace a ina kuka hadu dashi?

   Cikin dasheshshiyar murya tace layin makarantar mu"

    Juyowa yayi da sauri ya kalleta, akwai alaman tsoro a jdon shi, yace Allah yasa baki watsar da mutunciki ba ?

    Karuwa kukanta yayi, cikin kuka tace... Wlh bakomai Abba"

  Tsayawa yayi ya gama kare mata kallo, sannan yajuya ya fara tafiya tare da cewa daga yau karki sake fita ko haraban gidan nan bance kije ba,

   Juyawa yayi ya fice abinshi"

   Ma'u ko kuka taita yi, tana share hawayen"

    Da daddare mama ta shigo dakin ma'u ranta abace, ganin haka yasa ta takara shiga cikin hankalinta"

   Mama kasa mgn tayi illa kallo kawai data bita dashi, bayan ta gama kare mata kallo, ta juya ta fita batare da tace komai ba"

Washegari ma'u tanason ta sanar da deeni, ta rasa ya zatayi, gashi abba ya hata fita, kuma gashi bata taba karban no deeni ba, dan haka ta yanke shawaran ta rubuta taba drive ya kai mai"

   Bayan ta gama rubutawa, ta miki tana tunani yama zatayi tabawa drive, bayan abba yace ko haraban gidan be amince taje ba"

    Goggo tani ce ta fado mata, dan haka taje ta sameta, cikin ladabi tace mata goggo daman sani nake son nabawa sako, kuma gashi Abba ya hanani fita"

   Mikewa tayi tana fadi.... to bari nayo miki kiran sa, hala laifi kikayi"

     Sani drive nazuwa ta bashi takardan sannan tamai kwatan cen gidan, ya wuce"

        💝💝💝
  *Wanene *Jamal* ?


*Jamal* shine d'a name farko agun alhaji inuwa manga, mahaifiyar shi hajiya Sadiya bafulata ce ta usuli, bayan haihuwan Jamal suka samu sabani wadda harta kaisu da rabuwa"

    Bayan rabuwan su ne ya aure hajiya asabe wadda ta haifan yarta guda daya Aisha, ran hajiya asabe besoba, taso ace namiji ta haifa, dan haka ta dauki tsana ta daurawa Jamal, Jamal yasha matukar wahala agun hajiya asabe wadda suke kiranta da mami"

    Tun daga kan Aisha bata sake samon haihuwa ba, dan haka tsanan Jamal yake kara ruruwa acikin zuciyarta, jitake tamkar ta kashe shi"

    Jamal yasha wahala bakadan ba, duk da cewa mahaifin shi attajiri ne, amman mama taki bari yaji dadi, ta kanainaye komai"

    Dan haka tun yana karamin ya taso dason ya zama soja, saboda yawan zaman kunci dayake, ya saba da zaman shiru, zama shi kadai be dameshi ba, kulum yana daki saboda mami bata barin shi ya sake, kullun ida ya tafi makaranta tun safe sai 6, daya dawo zai shige dakin sa, haka yasa bashi da abokin hira sai karan ce karan ce, aban garen addini ma ba,abarshi abaya ba kullum da subahi yakan karanta Qur'ani, dan haka tun yana karami yake da kaifin basira"

    Har tasowan shi karatun shi kawai yasa agaba, bayan ya kammala karatu ne hankalin Alhaji inuwa ya fara dawowa kanshi,

      Kuma lukacin ne ya lura dabi,un shi, sun canja, baya son yawan mgn, dan haka ya fara janshi ajikin shi, itama mami lokaci da ta fahimci yanzun ya mallaki hankalin shi saita fara sakar mai fuska, agaban idon shi"

   Itako momyn jamal bayan rabuwanta da alhaji inuwa ta aure wani attajiri har suka haifi 'yarsu 1 Nafisa, sheran Nafisa 14 mahaifinta ya rasu dan haka bayan Momy ta gama takama ta dawo gidan alhaji inuwa, ayanzun haka shekaranta 2 da dawowa gurin daddy Jamal, tare da 'yarta Nafisa,

    Bayan Jamal ya fara aiki ne akafara mai zancen aure, amman ko kunya bayaji yake cewa Allah ya kyauta nine Zanyi aure, 'yar karamar yariya ta rainani, ni ba auren da zanyi"

    Lokacin daya fara fadin haka, daga Momy har daddy dariya suka yi, tare da ganin wauta ce ta mai yawa, hartakai duk abokan shi sunyi aure, amman shi ko abokin shine zaiyi aure daga gun daurin auren ya keyin sallama acewan shi bazaije gun taron mata ba haka kurum su raina shi, dan haka lokacin da usman ya matsawa Jamal ya kawo musu ziyara, yace zaixo amman fah bazai sauka gidan shiba sabo da kar matar shi ta raina shi"

     Dariya kawai usman yayi sannan yace toh kazo saika sauka gidan abba, haka tasa dole yayi karyan matar sa tayi tafiya"

   Acikin abokan Jamal babu wadda besan halinsa ba nashegen son girma"

  Momy da daddy suyi mgn har sun gaji akan yayi Aure amman killum mgnr daya ce, shifa bazaiyi Aure ba dan kada yariya tace zata raina shi"

     Tun daddy da momy nawa abin dariya, har yazo ya fara basu haushi"

    Ranan daya dawo daga gidan su ma'u kuwa kasa zama yayi, bashi falo bashi dakin momy, hakanan yaji zancen auren ma'u ya dame shi"

   Momy ce ta lura zirga zirgan shi yayi yawa dan haka ta bishi da kallo tare da fadin kai lafiyan ka ?

   Kusa da Momy yaje ya zauna sannan yace Momy wata 'yar tatsiyar yariya ce wai za,a mata aure, idan kika ganta kamar 'yar tsana"

   Tsaki momy taja tare da fadin kaifah baka da kan gado, na kula adawa kake da aure"

     Momy wlh yariyar da kadan tafi Nafisa"

    Hmmm Jamal kenan toh ai ko Nafisan ana iya mata aure, lallai ma Jamal kaman Nafisan kake kira 'yar tsana, Allah ya shirye ka"

     Haka ya kwana bayajin dadin, gashi ya rasa me yake damun Sa, dan haka washegari ya tashi bayajin karfin jikin sa"

   Gajiya yayi da kwanciya adaki karfe 11:30 ya tashi ya zauna abakin gadon, azuciyar shi yace waini meke damu na ne?  Husna yaji wani bangare na zuciyan shi na fadi"

   Tsaki yaja afili yace.... Babu wata *Husna* kawai ban da lfy ne, ji yayi kaman yanajin sanyi gashi har yanzun beji natsuwa tazo masa ba, dan haka yajawo bargon daya rufa dashi ya rufe jikinshi ruf, kanshi kawai kake hangowa ya nufi part din momy"

    itako momy tana zaune afalo, Nafisa kwance ajikinta tana kuka ahankali"

    Cikin tausayawa mama take cewa haba nafisa ki dinga hakuri mana, yakamata ace yanzun kin saba tunda duk Wata haka yake miki"

    Daidai lokacin mama ta hango Jamal yana tahowa ya kudundune cikin bargo"

    Da mamaki take kallon shi, harya karaso daf da ita ya zauna bata daina kallon shi ba"

    Menene haka kuma Jamal?

  Momy wlh bani da lfy"

   Allah na gode maka, meke damun ka?

    Yana kara lullube jikin shi yace... Inaji dai kaman zazzabi ne"

   Toh Allah ya sauwake, ka tashi ka koma daki kasha magani, kaga Nafisa ma tun safe mata jin dadi"

    Kallonta yayi sosai sannan yace.... Nakoma daki fah kikace, nace miki bani da lfy kuma kice na koma daki na zauna ni daya?

    Hmmm Jamal kenan, toh idan ka zauna anan ni me zan maka, kaga amfanin iyali kenan"

   Shiru yayi yana girgiza kai, zuwa can yace..... Momy nida Nafisa akwai banbaci kenan tunda gashi kin dauki nafisa kin daura ajikin Ki, nikuma kince nakoma daki,nayi jinyan kaina"


   Tunawa momy tayi da kishi irin na jamal dan haka ta fara kokarin daga Nafisa tana fadin zo ka hau"

  Mikewa yayi cikin sauri yana kokarin fita yana fadi, ai kince na koma daki idan na mutu shi kenan"

    Yana wucewa momy tace Ja'iri duk yadda akayi zama shi daya ne ya soma damun shi, bari dai daddyn sa ya dawo asan abinyi"


         ****


KANO



   Tun da sani ya tafi ma'u ta koma dakinta tana zaman jiran dawowan sani tare da addu'an Allah yasa komai ya tafi daidai 🙏🏻"

    Lokacin da sani drive ya isa gidan da asma'u ta kwatan ta mai fitowa yayi yai sallama akofar gidan"

   Ummi ce ta leko bayan sun gaisa yace....          Shamsuddeeni yake yake son gani"

   Kaman daman jira yake, ya fito yana mazurai, jada baya sani yayi domin tsorata da yayi da ganin deeni"

   Cikin mazurai deeni yace..... Kai!! Menene lfy?

   Jikin sani na rawa ya ciro takaddan ya mika mashi,tare da fadin asma'u ce tace nakawo maka"

   Murmushi ne ya baiyana afuskan deeni nan take ya warware takardan ya fara karantawa, bayani tamai akan kiran da abbanta yake mai, dadi yaji ba kadan ba, idon shi ya dago ya kalli sani sannan yace shikenan kace mata ina gaisheta, Jim yadanyi sannan ya juya zai shiga yana fadin inzuwa"

    Sani ya dade tsaye akofar gida yana jiran deeni, zuwa can saiga gashi ya fito, takarda ya mika masa sannan ya nuna masa hanya tare da fadin ware"

   Ahanya babu abunda sani yake banda tunani, tun da yake betaba tsam manin asma'u zata saurari mutum irin deeni ba, duba fah wai ni yake nunawa hanya saikace bani na kawo kaina ba, irin su abu kadan zaka musu su rufeka da duka, addu'a ya fara yi azuciyar shi Allah yasa kar akara aiko shi"

     **

  Deeni yau ji yake babu ishi, wani mugun farin ciki ne yaji ya kamashi, ummi ma taji dadin lbrn saidai ta wani  bangaren gabanta na faduwa, dan ayadda taga ma'u tasan cewa iyayenta bazasu so dabi'un autan ta ba, dan haka daga deeni har asma'u tana tausaya musu, dan itace sheda tafi kowa sanin inda suke son junan su"

    Zama tayi ta zuba uban tagumi tana bin deeni da kallo sai murmushi yake yi, hakan nan taji yana bata tausayi"

    Gyaran murya ummi tayi sannan tace.... toh auta goben kai kai kadai zaka ?

   Toh ummi nidawa zani, saidai idan idan caka zan kira, kai ninafison na tafi ni 1 "

    Da Sauri ummi tace eh gare katafi kai kadai, kuma dan Allah kayi shiga na mutunci karkai irin shigar nan taka, ni kaga asubanci zanyi domin inason nayi mgn da yaya larai"

Bece mata komai ba ya mike ya shige dakin Sa"

    Itako ma,u tunda sani drive ya kawa mata sakon deeni karantawa take tana sake maimaitawa, dadi taji dataga no banshi aciki dan haka bata bata lokaci ba wajen kiran shi"

   Da wayar mama ta kirashi dan ita har yanzun ba,a bata damar rike waya ba"

    Hira sukasha sosai sannan ta gaya mishi lokacin da abba yake gida"

    Goggo tani ta samu ta roketa dan Allah ta gayawa mama bakon nata zaizo gobe da misalin 11:30am"

    Dan haka washegari ta tashi da tunani guda 2, ko nasara ko akasin haka"

    Aban garen deeni ko, shiri yake tayi domin zuwa ganawa da sirikin shi, tun da duku2 ummi ta wuce dan haka shikadai ne agidan"

   Bayan yayi wanka ya gama kintsa jikin sa, karamar riga ya dauko hannunta iya daidai kafada, sannan yasaka wandon shi ya dan wuce guiwa da kadan, turare ya dauka yana fesawa ajikin shi, sai alokacin mgnr ummi ta fado mishi, da take cewa... idan ka tashi tafiya kasa kayan mutunci, kallon kayan ya kara yi sannan ya kalli gurin dayake ajiye kaya, gani yayi duk acikin kayan wannan ne me dama dama, dan haka ya saki fito tare da dage kansa sama"

   Fitowa yayi ya rufe gidan ya fara tafiya, ji yayi kaman akwai abinda ya manta agida, jayayi ya tsaya tare da shafa wuyan shi, sai lokacin ya tuna
ya bawa ma'u sarkan shi, da yanzun ita zatamai rakiya yana tafiya tana kara, tare da tashi sama, tsaki yaja afili yace.... Ina bazai yuyoba tafiya babu sarka kuma babu duna ai sai na dade banje ba"

Hannu yasa aljihun shi ya ciro waya sannan ya karata akunnesa
   yana fadin...... Caka kawomin Duna da matar sa zasumin rakiya"

    Cikin kankanin lokaci Caka ya kawa su kamar yadda ya bukata"

    Cikin wani irin taku ya fara tafiya duna da matar sa nabin shi abaya suna mishi haushi duk inda aka kan shi kyaucewa ake abashi hanya.....




  Heart Beat
*Mmn Yazeed*
[12/10, 8:16 PM] ‪+234 810 828 9060‬: 💗💝💝💗
​*BUGUN ZUCIYA*​
   ( ​Heartbeat​)

                   💓💝💗
                        💗           

💓💝💗
​By​
     💗
    ​​*Fadeela Lamido*




*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*




*💝💝💝 Salam masoya BUGUN ZUCIYA, hakika kun nunawa wannan book kauna, tare da ni kaina, farin cikina bashi missaltuwa, sai dai nace muku nagode2 Irin sosai!!! din nan, kuma ina fatan kun fara fahimtan darasin dake ciki💝💝😘😘*


*SADAU👇🏻KARWA*

*Masoya BUGUN ZUCIYA aduk inda suke*😍😘



   
         3⃣6⃣to3⃣7⃣




🐕🐕🐕 Cikin wannan yanayi deeni ya isa kofar gidan su ma'u"

    Yana kokarin taba get din sani drive na fitowa"

   Wani mugun faduwan gaba yaji dan haka besan sadda ya kauce ya bashi hanya ba"

   Mannewa yayi ajikin bango tare da bin karnukan da kallo, har suka shige cikin haraban gidan"

    Suna shiga gidan karnukan suka daina haushi sakamakon hannu da deeni yasa yana shafa musu kai"

     Zuwa can deeni ya dago ya kalli sani cikin daure fuska yace..... Gaya mata na iso"

   Jikin sani na rawa ya nufi cikin gidan, mama ya samu afalo jikin shi na rawa yace wai bakon Asma'u ya iso"

    Tabe baki mama tayi sannan tace toh ka bude masa falon alhaji"

    Juyawa sani yayi badan ransa yaso ba"

    Sani nagaba deeni nabinsa abaya, har suka isa, kofar ya bude, tare da fadin bismillah"

   Shigewa deeni yayi, su duna na take mushi baya' tsaye yayi yana karewa falon kallo, tare da fadi azuciyar shi, lallai mahaifin ma'u me kudi"

    Waiwaigawa yayi ya zabi kujeran dayaga tamishi ya zauna"

   Yayin da karnukan shi suka kwanta agefe"

    ***

Ma'u tunda taji sani yana gayawa mama ta shiga damuwa tare da addu'an Allah yasa deeni manyan kaya ya saka, kuma Allah yasa ummi ta gargade shi ya gyara harcen sa"

   Addu'oi da tai tayi kenan, har zuwa lokacin da taji fitowan abba da baba"

    Cikinta taji ya kada dan haka ta tashi ta shiga bayi"


    Alhaji musa ne agaba abba na binsa abaya dan haka alhaji musa na tura kofar yayi to zali da duna"

    Tsayawa yayi cak sannan ya juya ya kalli abba tare da tambayan shi, Gamo nayi ne?

   Atare suka maida idon su cikin falon, tare da karasa shiga ciki, ko wanne su bakin shi dauke da addu'oi a bakin shi"

     Wani irin BUGAWA ZUCIYOYIN su yayi atare ganin matashin saurayi zaune, karnuka kewaye dashi, cikin bin bango abba ke kokarin shiga ciki hannun shi daya dafe da saitin ZUCIYAR shi"

    Alhaji musa ne yayi karfin halin karasawa gaban deeni tare da fadin.... Daga ina?

   Deeni cike da kwarin guiwa yace nine bakon da Asma'u ta sanar muku da zuwan shi"

    Runtse Ido alhaji musa yayi tare da dafe kirjin sa yana sauke wani irin nufashi, ja yayi da baya ya nemi wata kujera ya zauna"

  Abba kuwa yana rike da kirji shi acikin zuciyar shi ko fadi yake Allah Yasa yazamto mafarki ne"

   Ganin inda Abba ya sandare aguri guda, yasa alhaji musa dakewa, ya fara kwalawa Asma'u kira"

    Tunda asma'u ta jiyo irin kiran da baba yake kwalawa tasan akwai Marsala, dan haka jikinta narawa tafi falon abba"

   Tagaban Abba ta wuce haryanzun yana nan a inda yake"

   Gabantane yai wani mummunan faduwa ganin duna kwance atsakiyan falon mahaifinta"

    Ganinta kawai tayi ta daura hannuwanta 2 aka, tare da zubar da hawaye"

   Sauke hannun ki taji Abba yace, bashiri ta sauke su kasa sannan tabi Abba da baba da kallo"

   Deeni ko ma'u yake kallo fuskan shi dauke da murmushi"

   Ahankali Abba ya nemi guri ya zauna, alhaji Musa ko, kallo yake bin ma'u da deeni dashi"

    Abba ne ya kalleta sosai sannan yace.... Asma'u wannan shine yaron da kikace kina so ?

   Eh, tace batare dajin kunya ba, dan ita ganinta wannan itace daman ta na karshe"

   Girgiza kai Abba yayi tare da fadin yayi kyau, shiru yayi zuwa can ya sake cewa.......Asma'u kikace wannan shine wadda kika amince ya zama uban 'ya'yan ki ?

   Kasa mgn tayi hawaye na zuba a idon ta"

   Shiko deeni, wani irin kallo yake yi Wa abba dan ya rasa inda mgnr abba ta nufa be amince bane, koko so yake ya tabbatar?

    Inajin Ki abban ya sake fada"

    Ahankali ta daga kai alamar eh"

   Abba komawa yayi ya kwanta ajikin kujera"

  Alhaji Musa ne yayi ajiyan zuciya sannan ya juya ya kalli deeni yace......... To kai Yaro bamu gaisa ba bare musan sunan ka"

   Cikin murya nan da kukasan deeni da ita ya karkace baki yace..... Sannu ku dai, ina kwanan ku?

   Alhaji musa ne kurun ya amsa Abba ko inbanda binshi da kallo ba abin daya ke"

   Cigaba yayi da fadin...... Ni sunana shamsundeeni amman anfi sanina da shamsun duna"

     Yayi kyau alhaji musa ya fada, sannan ya kara da cewa...... Kai dan gidan waye ?

   Murmushi deeni yayi sannan yace...... Ni jikan isa kaka ne"

   Isa kaka ? Abba ya fada yana zare ido"

    Eh, deeni ya fada"

Isa kaka ai 'ya daya ya haifa, kananufin kai dan saratu ne?

     Eh deeni ya sake fadi"

   Toh, toh, abu yayi na fahimta, cewar abba yana kokari mikewa tsaye, kanshi ya daga sama sannan yacewa alhaji musa shike nan, sallame shi"


    Ma'u alhaji musa ya kallah, sannan ya kalli deeni yace...... Shikenan kaje zamu neme ka"

   Mikewa deeni yayi yanabin ma'u da kallo ya fice waje, yan rakiyan shi nabin shi abaya"

Mikewa asma'u tayi zata fita, alhaji Musa yace koma ki zauna"

  Jikinta na bari ta zauna, abban najin fitan deeni ya kalli ma'u idon shi jawur yace..... tirrrrrr Asmu'u, kinyi asara, dan yatsan shi daya ya daga sama sannan yace wlh wlh Asma'u ko zaki mutu asma,u bazaki aure yaron nan ba"

   Alhaji musa ma mikewa yayi cikin tuhuma yace...... Asma'u kisan waye shi?, kinsan waye ubanshi?,
meye abin sha,awa?, me kika gani ?, meye ya rudeki ?

   Kan asama'u akasa kuka kawai take, kaman ranta zai fita, tasani dabi'un deeni basu da kyau amman tamai fatan shiriya, dan haka acikin zuciyarta take addu'an Allah ya karkato da hankalin su abba su bata zabin ranta"

   Muryan Abba taji ashake yana cewa..... Sabo da wannan abon kika kora mutane masu mutunci ?, Atunanin ki nizan daukeki inbawa wannan katon Dan iskan ? Wlh kinyi kuskure, baki isaba kinyi kadan, wato ina nan ina tufka wani na warware min" wan nan yaron da kike gani daga uwar shi har uban shi ba mutanen kirki bane"

   Yadda abba ke daga murya yasa mama shigowa tsaye tayi tana sauraran su, harta fahimce akan abun da suke mgn"

   Ma'u tabi da kallo hawaye ciki da idonta, Abba ko banda tsiyaya fada babu abinda yakeyi"

   Alhaji musa ne ya tsaidashi ta hanyar fadin......barta haka, yanzun mgn ta kare, bazamu zuba mata ido ta zubar mana da mutunci ba, ko kina so ko baki so da yardan Allah bazaki wuce sati 2 agidanan ba, za'a daura miki aure da duk wadda Allah yasa shine Mijin ki"

   Rikecewa ma'u tayi da kuka harta fara fita cikin hayacin ta, cikin kuka tace baba, dan Allah kumin rai, wlh Abba shi nake so, idan ban aureshi ba mutuwa zanyi, dan Allah karku rabani dashi, Allah ne ya dauramin sonshi bani nadaurawa kaina ba"

   Hawayen takaici ne suka fara zobowa a idon Abba, mikewa tsaye yayi azafafe ya fara takowa gabanta tare da fadin zakiyi fito nafito da ni ne ? yau zan gani tsakanin ni dake waye ya haifi wani, duka ya rufeta dashi kan kace me abba ya kece da amai"

    Alhaji musa arude ya nufeshi ya rike shi, amman duk da haka abba dukan ma'u yake tare da wani irin tari sai lokacin Alhaji musa ya lura kanin nasa aman jini yake"

   Daker ya rabashi da jikin ma'u duk jikinta jinin abba ne, haka yasa hankalin shi ya kara tashi"

    No Usman alhaji musa ya kira, ya gayamishi halin da ake ciki"

    Da taimakon Sani drive suka saka Abba amota suka nufi asibiti dashi"

    Shiko usman lokacin da akirashi suna tare da Jamal a Abuja, suna tsakiyar aiki"

   Ganin inda hankalin shi ya tashi yasa Jamal be bashshi ya taho shi kadai ba"

   Sun iso Kano dafda magariba, kai tsaye asibitin suka wuce"

    Lokacin da sukazo abba baya cikin Hankalin sa, kwance kawai yake, komai na jikin shi baya motse, bakin shine kawai yake motsawa, ahankali yakai kanshi saitin bakin abba, jiyayi yana fadin Asma'u, fadi yake baya kyaukyautawa, dan haka ahargitse ya kalli mama tare da fadin duk yadda akayi asma'u ce sanadin ciyon nan na Abba, bakin shi sunanta kawai yake kira"

   Sallaman dada ne ya katse musu hanzari, arikece ta wuce usman tana leka fuskan abban, ganin shi haka yasa ta fara tofamai addu,io"

   Usman ne yaci gaba da tambayan mama ma'u tayi wani abu ne ?

     Mamatana share hawaye take gaya musu halin da ake ciki, ai ganin dada kawai sukayi ta zame kasa, tare da fadin yanzun nan yariyar nan bata bar mgnr yaron  nan ba?

   Duk abinda suke Jamal na gefe yana kallon su, rungume hannun shi yayi akirji tare da lumshe ido kamar besan me ake cewa ba"

    Nan danan jikin dada ya rikice, haki ta fara babu kyau2 tawa dan haka usman yaje ya kira likita, cikin mintocin da basu wuce 7 ba, dada ta fita cikin hayyacinta dole tasa aka bata gado"

    Mama da momy ne suka kwana akan dada yayin da Alhaji Musa da su Jamal suka kwana akan abba, babu bacci dan Abba sai kusan asuba ya samu bacci"

       *****


Washegari Abba ya tashi jikinshi yayi dama dama bakaman jiya ba, saidai jikin dada sai kara rikicewa yake"

 
    Da misalin karfe 1:23pm Alhaji inuwa manga ya iso duba jikin abokin shi"

    Bayan gaishe2 tsanin alhaji inuwa manga da alhaji musa, matsawa yayi gurin Abba"

    Mgn suke ahankali abba da kanshi yabawa alhaji inuwa lbrn halin da ake ciki"

Nasiha yamai tare da tare da kara bashi shawar wari, nan Abba yadan ji sanyi aranshi"

    Zuwa can abba yaji bacin rai ya sake taso mai, dan haka ya kira jamal da usman yace musu..... Maza kuje gida kutaru Ku karya min asma'u"

   Kaman jira suke suka fita cikin sauri, Alhaji inuwa nakiran su ina, sun riga sun fice"

    Bayan fitan su alhaji inuwa yakalli alhaji musa yace inason ganin ka"

    Waje suka fita sun dan juma sannnan suka dawo fuskan su dauke da murmushi"

    Abba kallo ya bisu dashi, koda besan me suka tattauna ba, ya san magana ce me mahimmanci"

    Ganin inda yake kallon su, yasa alhaji musa cewa......rana ita yau za,a daura auren *Asma,u* da *Jamal* mahaifin shi ya neman mai aureta aguri na kuma na bashi"

   Cikin farin ciki Abba yace Allah ya nuna mana"

 
*****


Ma'u ko yadda taga rana haka taga dare ba abun da yake damunta ban da tunanin abban ta, kasa komai tayi nan danan ta rame tai zuro2 goggo tani ce taita lallashin ta ruwa kawai take iya sha"

   Misalin karfe 3:00 goggo ta matsa mata tai wanka, dan haka ta mike ajikinta babu kwari tacire kaya ta dauko towel ta daura, toilet ta shiga harta tube ta murza kunfa, tafarajin ana kwala mata kira, cikin hargagi, muryan yaya usman ta gane aciki, hayaniya irin nasu na sojoji"

    Arikece ta mike ta dauki towel dinta ta daura, daidai lokacin taji an banko kofar daki"

   Saida ya kira sunanta so uku ajere sannan asma'u ta amsa adabur ce"

    Fito dan uban ki"

   Cikin rawan murya tace yaya wanka nake yi"
 
     Idan kika bari nashigo bazan miki da wasa ba"

   Kara rikicewa asma,u tayi, sannan ta rushe da kuka, batai aune ba taga yaya usman acikin bayin, mari ya wanka mata, kafin ta ankara take karajin saukan wani, dan haka ta riki ce tayi waje rike da towel dinta dake kokarin warwarewa"

    Mutum take gani dishishi kamar yaya Jamal zaune agefen gadonta cikin kakin sa, yana danna waya"

     Gani tayi ya rabun mata kashi2 duk inda ta waiga shi take gani, daga can ta hango yaya usman yayo kanta, Dan haka aguje ta tayi kan abin da take ganin shi kaman gizon yaya jamal





 
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
[12/10, 8:16 PM] ‪+234 810 828 9060‬: 💗💝💝💗
​*BUGUN ZUCIYA*​
   ( ​Heartbeat​)

                   💓💝💗
                        💗           

💓💝💗
​By​
     💗
    ​​*Fadeela Lamido*




*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*




Dedicated👇🏻
   *Miss xoxo*
I love u, so much😘
*Kaunarki gareni daga Allah ne*



      3⃣8⃣to4⃣0⃣



🤺🤺🤺



🤺 Duk da cewa Jamal yayi kaman beganta amman yana ganin inda ta nufoshi gadan2 yasa ya ajiye wayar shi agefe sannan ya miki cikin sauri"

  Itako asma'u tanazuwa ta fada jikin shi ko da tajita jikin shi ma, bata tsaya ba, kara kadandane shi take dan tasan idan tayi haka dole yaya usman yabarta, dan haka hannunta tasa  guda 1 ta bayan sa yayin da dayan ta danne towel dinta dashi"

  Ganin haka hankalin Jamal yayi mummanan tashi kokarin rabata da jikin shi yake tare dasa hannushi ya rike mata towel din kamar yadda yaga tayi, saboda gudun kartayi tsirara, cikin tsawa yake fadin usman bari, bari, menene haka ?"

   Usman natada jijjiyan wuya yake fadin..... kasan Allah wlh saina sumar da yariyar nan"

   Shima cikin tsawa yace naji ko ka shetama zakayi zaka iya amman ka bari tasa kaya ajikin ta"

    Usman fah ranshi ya riga ya bacci banda jijiyoyi kan shi baka hango komai, dan haka jamal ya dauketa cak ya nufi toilet da ita, tare da kare dukan da usman yake kaimata"

   Ciki ya sakata sannan ya jawo kofan tare da tsawa abikin toilet din dan usman har yanzun be hakura ba"

   Kallo Jamal yabi usman dashi sannan yace dallah jin inda kake tada jijiyan wuya, mace ce fah, macen ma yar ficiciya"

    Juyawa usman yayi yana huci, ya fice"

   Usman na fita jamal yaja tsaki sannan yace ke kuma dallah karki cikawa mutane kune da kuka, nan dan ma'u ta kunshe bakin ta"

   Zuwa can ya sake cewa fito ki saka kaya, ki fito falo ki same ni"

     Sai da taji ta dainajin motsen sa sannan ta fito, tayi zuro2 da ita"

    Saboda tsabar rudewa riga daban siket daban ta Saka, sannan ta daura Karamin hijjabi akai"

    Afalo ta same su, Usman har yanzun bebar huci ba, Jamal ko kallo ya bita dashi, Sannan yace tsuguna kisa guiwar ki akasa"

    Tsugunawa tayi kamar yadda yace tare da sunkuyar da kanta kasa"

    Daga hannun ki sama sannan ki rufe idon ki"

   Innalillahi, ta fada sanan ta miki tana dan bubbuga kafa alamar tsoro"

   Mekewa jamal yayi tare da fadin eh lallai baki dakuba, rawa ma kike min ?

  Cikin kuka ta tsuguna tana fadin wlh na daku, hannu nama ciwo yake min dan Allah kuyi hakuri"

   Usman ne yace nagaya maka duka ne ya dace da yariyar nan, kace ba haka ba, mikewa yake kokarin yi Jamal ya tare shi tare da fadin banni da ita, karyan rashin kunya take"

   Dasauri ma'u ta tsuguna tayi kamar yadda yace, idonta arufe amman hawaye  na zuba a idonta, bayan kusan minti 30 taji daya daga cikin su ya fita, saidai bata san ko wanene ba"

   Gaba daya jijjiyoyin hannunta ya sake, kuma hakan takejin kamar kallonta ake dan haka tayi saurin bude ido"

    Jamal ta gani ya ya kurawa guri daya ido, bin inda yake kallo tayi da idonta, nan ta gane ashe sanadin daga hannunta sama rigarta ta daga dan haka cibiyanta baiyane yake, kuma indai idonta ba kizo ya mata ba' Jamal gurin yake kallo"

    Cikin sauri tasa hannunta ta jawo siket dinta sama, zabura Jamal yayi tare da fadin ke!! Waye yace ki bude idonki"

    Mayarwa tayi ta kulle, tare da kara tsanan Jamal, tsine mishi taitayi azuciyanta tare da mai fatan bala'i kala2, bata san abin da yasa ba, duk abin da yaya usman zai mata kadan yake bata haushi, amman na jamal yana mata kuna"

     Saida Jamal yaga tana tangadi kamar zata fadi sannan yace zauna"

    Zama tayi tana share hawaye da hijjabinta, idon nan luhu2

  Wuce kiban waje kuma duk ranan da kika sake Tayar da zancen me kare sai kinci kaniyar ki"

   Tafiya ma'u tayi harta shege daki tana jerawa jamal Allah ya isa, tare da addu'an Allah yasa yana fita mota ta begeshi ya mutu"

    Har Washegari su mama basu dawo ba, dan haka taji bazata iya hakuri ba, Sani ta samu ya dauketa suka tafi"

    Tunda sani ya sauketa gabanta ke faduwa ba komai ke damunta ba sai haduwanta da Abba da mama, tasan suna fushi da ita"

   Tana tura kofar dakin sukai idon 4 da mama, daga can gefen gadon ko, wani Mutun ne, me tsananin kama da Jamal sosai kamar harta baci"

    Mama na ganin ma'u ta mike tana fadin.....

    Me kikazo yi ?, menene ya kawo ki?, kinzo ki karasa su ne ?....

   Sakin kofar ma'u taso yi, karafff taji anriketa, wannan mutumin ne me kama da yaya Jamal"

   Hannnuta ya ruko suka shigo cikin dakin, sannan ya kureta da ido, zuwa can yace a shema yariya ce karama, rashin wayo ne yake damunta, kallonta ya karayi sannan yace..... Yi shiru kinji 'yata? Ki daina kuka"

    Ta gaban mama ya wuce da ma'u agaban gadon da abba yake ya saketa sannan yace...maza ki tsuguna kibawa mahauifiki hakuri, nasan kinje makaranta kuma kinsan girman iyaye agare ki, daga yau kar akara ce miki ga abinda zakiyi, kice a'a, domin duk abin da babba ya hango yaro ko rimi yahau bazai iya hangowa ba, kuma wani lokacin zuciyarmu nason abu, wata kila ba alheri bane, dan haka kiyiwa iyayenki biyayya, ko kinason wani abu ya samu mahaifin ki ta dalilin Ki,?

    Gargiza kai ma'u tayi hawaye na sauka aidonta"

    Toh ki maida hankali Ki, gatan da uba zaiyiwa yarsa shine aure, kuma wada duk ya rasa wadda zai masa fada yayi asara"

    Sosai maganga nun suka shiga jikin ma'u, cikin kuka tafara rokon Abba gafara, tare da nuna masa yayi yadda ya gadama da ita"

  Koda abba bece mata kallah ba Amman yaji dadin kalamanta"

   Alhaji inuwa kan mama ya juya yaita nuna mata mahimmanci jawo 'ya'ya ajiki, tare da nuna mata ta daina kyaran ma'u"

   Bayan ya gama da mama ya sake jawo hannnun ma'u ya kaita har dakin da dada take, saidai dada naganin ma'u ta fara fadin Innahu Sulaimana Wa innahu Bismillahir Rahimu, Kalu lahaula, Lahaula wala kuwata, kufita min da ita , gata nan, gata nan"

Momy ce ta rike dada tana fadin dada Asma'u ce fah, takwaranr ki, ki kwantar da hankali ki mana"

   Karasawa daddyn Jamal yayi ya kamo hannun dada ya hada dana ma'u, sannan yace mata ta bata hakuri"

   Cikin kuka ma'u ta rike dada tace dada kiyi hakuri dan Allah nina bari bazan kara ba"

   Arikece dada tace kikace kin bari, kin hakura dame karan?

    Kai ma'u ta gyada mata"

   Ke takwara da gsk kincire me karan azuciyar ki?, nidai indai kinsan baki hakura ba' to ki fada min, dan nasa amai dani mahaifata"

   Hannu tasa ta share hawaye sannan tace nahakura dada"

   To ko kefa, yanzun kinga ran juma'a za'a daura miki Aure"

   Gabanta taji ya fadi rasss, sakamakon jin zancen dauren aure, amman yaya zata yi indai tana son zaman lfy, dole tabi umarnin iyayenta"

      *****

  Kwanan su uku a asibiti suka dawo gida, Allhamdulillahi jiki yayi kyau sosai, kuma aranan abba ya sanar da ita ranan juma'a zai mata aure"

    Tadade zaune agaban abba tana kuka, ganin inda take kuka ya hana ya gaya mata waye mijin nata"

 
*Abuja*


*Jamal* ne zaune agaban daddyn sa, gefensa momy ce, duk kansu fuskan su babu wasa, hakan ne ya tabbatar masa mgn ce me mahimmanci daddy ya kira sa akai"

   Rubuce rubuce daddyn keyi akan wasu takardu, zuwa cen daddy yayi gyaran murya yace Jamal yau yaushe ?

    Tuesday ya fada yana kallon fuskan daddy"

   Batare daya kalleshi ba, daddy ya sake cewa toh ran Friday za'a daura maka aure"

   Azabure yace Aure kuma daddy? aini nace muku bazanyi aure ba"

    Bazaiyiwo ba Jamal Aure ibada ne, Allah Ta’ala da ya tashi ni’imtar da bayinsa daga rahamarsa, sai ya ni’imtar dasu da Aure, domin aure daya ne daga cikin ni’imomin Allah, wanda Allah ya ni’imtar dashi akan bayinsa gaba daya'
Kuma Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yace“ Idan bawa yayi aure, hakika ya cika rabin Addinin sa, sai yaji tsoran Allah asauran rabin,
Kuma ya kara cewa“ Duniya rayuwa ce mafi alkhairin rayuwar duniya mace tagari

Jamal  ka duba mafi yawa daga cikin wadan da basuyi aure ba, kuma suna da ikon yin auren, zaka ga tunanin su gaba daya kan Zina yake, kuma zina tana nisantar da mutum a yanke daga imani"

    Shiru Jamal yayi domin bashi da bakin mgn"

   Zuwa can daddy yace..... Jamal baka ce komai ba"

   Shiru yayi kaman bazaiyi mgn ba, zuwa can ya bude baki cikin fushi yace... daddy nifa raini ne bana bana so"

  Murmushi daddy yayi kadan, sannan yace..... kana bani dariya Jamal, ai ba kanka aka fara ba, bakuma kanka za'a kare ba"

   Shiru yayi zuwa can ya miki zuciyar shi cike da tunani kala2, babu abin da yake bashi takaici irin ace wai shine zaije yanawa yariyar daya girma karamar murya"

    Muryan Abba yaji yace baka tambaye ni amaryan taka, ko kunyi mgnr da usman ne?

  Cike da mamaki yace daddy usman yasanta ne?

  Murmushi abba yayi, sannan yace kanwar sa ce, Asma'u

  Afirgice Jamal ya daura 🙆🏼‍♂ tare da fadin haba daddy ya zakamin haka, sabo da Allah, daddy karasa yariyar da zaka hadani da ita sai asma'u, yariyar da bata da kunya, kuma ma ai ma ba tsarata bace, shekara ta 30 harda wani abu, ita kuma 10 da wani dan kwayoyi, haba daddy me zan  da ita, inbanda ta raina ni.....

   Gani daddy yayi bashi da niyar shiru kamar ma sambatu yake, dan haka ya mike sannan yace..... nidai nagaya maka, idan ka gaji da surutun ka bari"



    *Kano*


Tunda ma'u ta dan saki ranta, mama take dan sakan mata fuska, dan haka yau ma'u ta mamayi mama ta dauki wayarta"

   Dakinta ta shiga ta kulle ko ina, sannan ta fara shigar da no deeni"

   Kaman jira ya ke ya daga tare da fadin haba asma'u
Yazaki share ni kunsan kwana nawa kinsan halin dana shiga kuwa ?

   Kuka ne ya kwace cikin sauri tasa hannuta ta rufe bakinta dan gudun kar yaji kukanta"

  Marairaicewa ya sakeyi yana fadin asma,u bari na kwatanta miki yadda nakeji"
    Asma' na kasance tamkar kifi a cikin ruwa, idan nayi gabas sai kuma na dawo nayi yamma, idan nayi kudu, sai kuma na dawo nayi arewa"

    Shiru yaji, dan haka ya sake cewa asma'u me yasa kikai shiru ?

   Hannun ma'u dafe da bakinta, ta kasa cewa komai, tausayin deeni, tare da tsananin kyaunan sa takiji acikin jikin ta, hawaye da majina ne suka hade afuskanta"

   Shiru yayi zuwa can ya sake cewa..... Asma'u nasan kinaji na, yau kuma wani sabon salo kika fito dashi?

Shiru ya sakeyi zuwa can yaji shirun yayi yawa, dan haka yace....
   Tattausan lafazin ki nake saurare yake abin kyaunata, komai naki daban dana sauran 'yan mata, da zan kwana ina misalta kyawun halittar ki, ba zan iya kaiwa karshe ba, koda kuwa zan wanzu ina yi har karshen rayuwata"

    Kasa danne kukanta tayi, cikin kukan ta bude bakinta, domin ta faranta mishi rai, tana sheshshekan kuka take cewa.....
    Akwai matsala deeni"
 
   Wani irin nufashi yake fitarwa, kasa yayi da murya sannan yace..... wacce irin matsala kuma asma'u ? bakya so nane?

  Hannu tasa ta share hawaye da majinan dasuka dame afuskanta, sannan tace......
  Ina sonka tamkar yadda ba zan iya bayyana maka ba, ina sonka tamkar yadda baza ka iya kirga adadin ruwan sama ba, kada ka zubar da hawayenka, yayin da wani ya bata maka rai, tuna da wacce kake so, ka ke kauna, sai zuciyarka tayi fari, ina sonka abin kaunata, na kasance a cikin matsin kasa bacci yayin da dare ya tsala, bani da komai sai tunaninka har wani lokacin gari kan waye ban iya runtsawa ba, nasan wannan yana faruwa ne saboda irin tsantsar soyayyar da nake maka, Shin ko kaima haka ne?

   Karashe mgnr tayi cikin matsanancin kuka"

  Dan haka hankalin deeni ya tashi, idonshi ya kankance, karkace baki yayi sannan ya bude wannan muryan tasa yace wanne d'an ta shekiyan ne ya bata miki rai har kike kuka?

   Sau sauta kukan tayi sannan tace deeni ranan juma'a za,amin aure"

   Diffff yayi, zuwa can yace...... Yaseeeen karya ne, Asma'u ko sama da kasa zata hade hakan bazai faru ba"

   Itadai ma'u kuka kawai take"

  Jitayi ya sake cewa dawa za,ayi miki auren"

   Nima bansani ba amman ina zaton Jafar ne"

   Kai!!! Ina, yaseeen karya ne"









  Heart Beat
*Mmn Yazeed*

💗💝💝💗
​*BUGUN ZUCIYA*​
   ( ​Heartbeat​)

                   💓💝💗
                        💗           

💓💝💗
​By​
     💗
    ​​*Fadeela Lamido*




*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*




Dedicated👇🏻
   Faty Afreen💋🤳🏻




     4⃣1⃣to4⃣3⃣





💕💘💞💕​
Asma'u idan kika ga na barki agidan wani to ki tabbatar bana numfashi"

  Zan dauki mataki agun duk wadda ya nemi ya rabani dake, ke tawa ce danni aka halicce ki"

   Nisawa yayi yana huci, yaci gaba da cewa karki yadda da duk Wanda za,abaki, dan wlh zan kashe mutun"

    Shi tsohon naki bashi da anhali ne, zan batar dashi yaseeen'

   Kukanta ne ya Karu, cikin kuka tace......
kayi hakuri banason abin da zai taba abba na, duk abinda ka mishi ni kamawa, kuka ta tsaya tayi sosai, deeni yana sauraran ta, zuwa can tace.......
    Deeeni muhakura kawai"

   Diffff, yayi zuwa can yace...... Asma'u ni kike cewa muhakura? Kin manta kalaman da kika gayamin yanzu, daman yaudarata kikeyi ?

   A'a ba haka bane deeni, tunanin abbana nake, banason nasa shi awani hali, tunda ya nuna baya so, dole na hakura koda haka zai zama sanadin ajali na"

   Girgiza kai deeni yayi kaman yana gabanta sannan yace........
    haka kika ce ko ?, tabbas zan kashe Jafar"

   Iya abin da ma'u taji kenan ta kashe wayan, tare da fashewa da kuka, acikin zuciyanta tace wlh wlh duk wadda ya aure ne ya daukan ma kasan wahala, dan bazai taba samun inda yake so ba"

   Kuka tayi sosai sannan ta goge no deeni, toilet ta shiga ta wanke idonta sannan ta nufi dakin mama domin ta mayar mata da wayarta"

   Tana shiga mama tace idan kin gama da wayar bani "

   Bata nuna tsoro ba, cikin dakewa ta mika mata tare da cewa......
   Muyi hira da zainab ne, dan mun dade bamu hadu ba"

 Hmmm kawai mama tace, Sanan ta karbe wayar ta tare da fadin ga zuma nan a cup zauna ki shanye shi, ki bani cup din"

    Bata kawo komai azuciyarta ba ta zauna ta dauko kofin, rabon da tasa wani abu abakinta ta dade, deba tayi ta kai bakinta, wani irin bauri taji, dan haka ta mike aguje tayi toilet"

   Binta da kallo mama tayi, tanajin ta tana kwara amai, zuwa can ma'u ta fito tare da fadin mama, menene wannan kika bani ?

   Zoki zauna mama ta fada tana nuna mata wajen zama"

   Zuwa tayi ta zau sannan mama ta dauki cup tace bude bakin ki, wannan abun da kike gani yana da muhimmaci sosai, kuma kinsan bazan baki abinda zai cutar dake ba"

   Bude baki asma'u tayi tare da rufe ido mama taita dura mata zubar abaki, bayan ta gama mama ta kalleta, sannan tace..... Yanaga  idonki sun kara tasawa? asma'u kodai har yanzun jikan kakan nanan zaciyan Ki ne?

   Shiru tayi, mama nabinta ta kallo zuwa can tace niba tunanin sa nake ba"

   Toh tunanin me kikayi asma' u kinga yadda kika rame kuwa, kinyi wani zuro2 dake, jifa inda wuyan riganki ke fadowa"

   Kallon wuyata tayi sannan tace......

    Mama toh daza'a dan daga auren ne tunda yanzun banda lfy"

   Hmmm asma'u kenan, ai idan ma kina tunanin za'a daga auren nan gara ki bari"

   Shiru tayi zuwa can tace mama abba fah yamin alkawarin bazai min auren dole ba, kuma gashi zaimin."

   Ke kikajawa kanki asma'u ban da rashi tunani meya kaiki soyayya da d'an daba,  duk wadda kika ganshi awannan harkan bayajin tsoron iyayen sa, dan duk iyaye na gari bazasu so ganin dansu cikin irin wannan harka ba"

   Shiru sukayi zuwa can ma'u ta kalli mama tace......
    Wlh mama deeni yanada kirki, kuma inaji ajikina idan na aure shi zai bari, cikin rawan murya ta karasa dan haka mama ta bita da kallo sanan tace........
   Zuciyan Ki bata gaya miki gaskiya asma'u, ki daina asaran hawayen ki"

   Shiru asmau tayi bata sake cewa komai ba, saidai lokaci zuwa lokaci tana Saka hannunta ta share hawaye"

   Jamal kuwa tunda tunda yaji lbrn auren shi da asma'u ya rage walwala, baya wa kowa magana sai yaita mazurai yana cicin magani"

   Yau alhamis Jamal na zaune adakin sa yana aikin da ya saba wato karatun jarida"

    Ji yayi ana buga kofar, saida ya hada rai sannan yace waye?

   Nafisa dake tsaye abakin kofa tace... Nice"

  Shiko ya fada tare da maida kanshi kan jaridan"

   Shigowa tayi sumi2 harta nufi bakin gadon, ta tuna yaya Jamal baya son ahaumai gado, dan akwai Wata rana data zauna abakin godon yaita masifa, wai dan tsabar rashin kunya zata zauna mai agado, saida Momy tasa baki sannan yabar mgn, dan haka yau ta tsaya atsaye"

   Yaya Jamal ina kwana"

  'Dagowa yayi fuskan shi adaure ya kalleta, wanne irin iskanci ne zakizo kimin tsaye aka"

   Cikin sauri ta nufi kujeran ta zauna sannan tace, daman Momy ce tace naxo na dubaka ko lfy, wai taga tun safe baka fito ba, kuma abba na kiran ka"

    Toh naji, wuce kiban waje"

   Jifa yayi da jaridan hannu shi sannan ya miki yabi bayanta"

   Har cikin dakin daddy ya shiga, daga nesa dashi ya zauna ya mika gai suwa"

   Bayan daddy ya amsa sukayi shiru na dan wani lokaci, zuwa can yace......

    Jamal jibi fah daurin aure banga gana shiri ba"

 Daker ya bude baki yace.......
nasani ai daddy ni babu wani abu da zanyi ne"

    Toh ai ko bazaka yi komai ba Jamal ka gayawa abokan ka, ko baka son suzo maka daurin aure ?

   Shiru yayi bece komai ba"

   Kallon shi daddy yayi sosai yace.... Kuma gashi har yanzun bakaje gurin yariyar ba, domin kaji bukatun ta"

   Cafff ya fada azuciyan shi, afili kuwa sai yace, sai dai nayi aike daddy, dan inada aiki gobe"

   A'a, ai zuwa dakai yafi sako kadaure dai kaje din kaji ko"

   Toh kawai yace tare da mikewa yana kokarin fita, axuciyan shi yace.....
 yaya ma za'ayi nayi zaman aure da *Husna* ai ni koda anyi aure sai dai na aure wacce ta girme ni"

       ***




Deeni ko tunda suka gama waya da asma'u ya shiga cikin wani hali,  haka kurum yaji hawaye na zubo mai, tunda yake beta neman wani abu ya rasa ba, duk abin da yake so shi ake mishi, amman yau yaga ma'u na shirin subuce mishi"

    Cikin wannan halin ummi tacimai afirgice tace.....

    Auta menene haka? Meya maka zafi har kake tsiyayar da hawaye?

   Hannun yasa ya share hawayen sannan yace ummi zan kashe baban Asma'u, dan naga nema yake ya rabani da ita"

  Kul auta na karka soma, kana son ka tura mata kiyayyan ka ne ?, mundin ka kashe babanta toh duk son da take maka juyawa zaiyi ya koma kiyayya, kuma ina gargadin ka da kadaina kuka idan Allah ya yarda zaka Aure asma'u"

    Hannusa ya shafo hawayen ya kallah ummi wlh in masifar son asma'u"

    .Nasani auta tun da gashi naga kana zubar da hawaye rabonda naga hawayen ka tun kana goye"

 Ummi bakomai ke ta damin hankali ba, ummi sai kalman asma'u wai ta hakura dani sabo da bata son bacin ran abbanta, ummi to idan nakashe Mijin fah"

   Karka kashe kowa auta idan Allah yaso dakai za,ayi"


   ****


       Yau ta kama alhamis, dan haka baki sun fara sauka agidan su ma'u"

     Tunda ma'u taga 'yan uwan sun fara zuwa hankalinta ya tashi, tunanin ta gobe iyanzun tana matsayen matar wani, ba deeni ba" kuka take son yi amman hawayen yaki zuwa, rasa inda zata saka kanta tayi"

    Da misalin karfe 11:00am yaya usman ya shigo har dakin ma'u, fuskan shi daure yace ke dauko gyalen ki kisame ni amota"

 Mikewa tayi cikin sauri ta fito, ganin Anty fa'iza acikin motan yasa taji sanyi"

   Tunkafin ta karaso anty fa'iza ke mata murmushi, shiga tayi ta zauna, har sukai nisa babu Wanda yace uffam"

   Sunyi tafiya me nisa, sannan Anty tace, asma'u lalle zamu da gyaran kai kinga gobe dauren aure ko?

   Dauke kai ma'u tayi tare da matso hawaye, wani kululun abu taji ya tsaya mata awuya"

   Bata sake cewa kala ba, har sukaje akayi komai aka gama, ko ruwa aka bata bata sha"

  Bakaramin kyau ma'u tayi ba, lallai ne dan uban su, dan haka tai kaman ba itaba, sai dai raman da tayi yasa idonta duk ya zurzurma"

   Sun kusa isa gida wayar yaya usman ta fara kara,  dauka yayi ya kara akunne sannan yace ka iso ne?, OK toh kashiga ciki mana, shiru yayi zuwa can yasake cewa toh kama ka zasuyi?, tsaki yaja sannan ya kashe wayan"

    Karfe 5 da wani abu suka dawo, tun kafin ta fito ta hago yaya Jamal tsaye ajikin wata mota, gani tayi kaman ya kara tsayo dauke kanta daga kallon shi tayi, aranta take cewa shikuma wannan mugun meya kawo shi" wata zuciyar tace kika sani ko an gaiya to shine idan kinyi gaddama yaci uban ki"

    Batace zata jira anty ba tayi gaba abinta, koda taje gaban Jamal bata kalli inda yake ba, harta wuce Taji yaya usman na cewa ke zonan"

   Juyowa tayi afirgice tazo gaban su ta tsaya"

    Zakice bakiga Jamal bane koko gaidashi ne bazakiyi ba?

    Ban kula dashi bane, ma'u ta fada sannan tace ina wuni?

   Juyowa Jamal yayi ya kalleta, sannan ya tabe baki tare da daga hannu shi, ya mata alma wai tatafi"

    Koda tashiga gidan, kowa fadi yake tayi kyau, azuciyar ma'u fadi take da kusan abinda nakeji da bazakumin mgn ba"

  Zuwa can Anty ta shigo, fuskanta dauke da dariya ke kuma haka akeyi, kina ganin mijinki saiki wani dauke kai"

   Dasauri ta kalli Anty sannan tace waye mijin nawa ni ba wanda nagani"

   Hmmm Asma,u bayan tun muna cikin mota naga kin kalle shi"

   Mikewa tsaye tayi da sauri sannan ta koma ta manne da bango, hannunta dafe da kirjinta Anty kina nufin *Jamal*? Jamal ? shi abba ya hadani dashi?

    Mikewa anty tayi cikin sanyin jiki tace, daman baki sani ba?

   Innalillahi wa inna ilaihir raju'un, wlh bana son shi, bazan aure shiba, dana Aure shi gara na kashe kaina"

   Kafin anty tayi yinkurin cewa wani abu, ma'u tafita da gudu, cikin kuka tashiga dakin mama, idonta arufe ta fada jikinta tana kuka kaman ranta zai fita tace mama dagaske wai da yaya Jamal za'amin aure ?

    Kai tsaye mama tace, eh, daman abban Ki be gaya miki ba?

   Bana son shi mama, wlh na tsane shi, dan Allah karku hadani dashi, mugune mama, kuma azzalumi ne"

   Bakin alkalami yariga ya bushe asma'u, dama ki daina bata bakin ki"

    jikin bango ta koma ta dunkule hannu tare da fadin, mama wlh idan aka hadani dashi zan kashe shi, zan kashe mama"

   Batasan cewa yaya usman na dakin ba, saiji tayi yace" idan har zaki iya to ki kashe shi"

   Bataji tsoro ba, dan yanzu jitake zuciyarta ta bushe, da za'aita dukanta har akasheta dataji dadi"

    Dakinta ta koma ta zauna tare da zubawa guri daya ido, deeni ne ya fado mata arai, inama zabar ta ta aure deeni, dataji dadin arayuwan ta, Amman me ake da wani jamal, tsaki taja sannan tace afili , wlh idan har akayi kukkuren yimin Aure da jamal dagani harshi haka zamu kare rayuwan mu cikin bakin ciki"

   Tana cikin wannan tunanin taji ana kiran sallahn mangariba, mikewa tayi ta dauko dogon hijjabi har kasa ta saka"

   Lekawa falo tayi taga babu kowa duk sun shiga sallah, dan haka tacire ta kalminta tarike ahannu sadaf2 ta fice agidan"

   Gidan su deeni ta nufa tana tafe tana waige, harta isa gidan, akofar gidan ta tsaya ta kurawa dutsen da tasaba ganin deeni akai ido, hawaye taji yana zubo mata, ahaka ta shiga gidan, deeni na zaune atsakar gida ya zuba uban tagumi"

    Tsugunawa tayi agaban shi, ahankali ya dago ya kalleta"

   Mamaki baiyane afuskasa yace asma'u kece?
 
  Cikin kuka tace nice deeni"

   Yaya akayi kika fito da daddarenan ina nan ina shirya kayan yakin da zan fito dasu gobe, ina tabbatar miki gobe babu tsoho babu Yaro shara ne kawai"

  Hannu tasa ta rufe mai baki sannan tace, bazaka iyaba deeni, kasan dawa za'amin aure ?

   Gargiza kai yayi tare da kura mata ido"

   Jamal, tafada tana share hawaye"

  Wata irin muguwar dariya yayi sannan yace, jamal"?

   Eh Jamal, ka kwatar da hankalin ka, bazan taba zama da jamal ba, na yake shawara adaren da aka kaini aranan zan kasheshi, karkace zaka dauki wani bataki, ka bari harsai nakasa"

   A'a asma'u bazaki iya ba, insha Allahu bazakije kidan saba, ke macece bawani karfi gareki ba, ni kuma *na dad'e ina dama furata bazan so wani ya shanye min ba,* abin da yafi kawai kije gida da asuba kisan yadda zakiyi ki fito zanzo na daukeki mugudu"

   Shiru tayi zuwa can tace......

    Deeni wacce fura ce wannan?

  Kau da idon shi yaye gafe, tare da fadin bazaki gane ba"

  Cikin sauri tace nagane deeni, ummi na nan ne ?
 
   Daker iya cewa taje anso min magani"

   Shiru ta sake yi zuwa can ta kalle shi tace toh me zai hana kashanye furan taka yanzun"🙆🏼











Heart Beat
*Mmn Yazeed*

💗💝💝💗
​*BUGUN ZUCIYA*​
   ( ​Heartbeat​)

                   💓💝💗
                        💗           

💓💝💗
​By​
     💗
    ​​*Fadeela Lamido*




*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*



Dedicated👇🏻

*Firdausi Sodangi*💋




     4⃣4⃣to4⃣6⃣




🚔🚔🚔



Da saurin shi ya mika hannun shi kan kafadan ta, ido ya zoba mata, itama kallon shi take cikin ido"

  Sun kwashi tsoyon lokaci ahaka, zuwa can ya sake shigota"

   Asma'u nasha kika ce?

   Kai ta gyada masa sannan tace indai hakan zaisa ka yadda dani.....

   Bata gama rufe baki ba, ya rarumo bakinta, sunbatan ta yake kaman zai cinye ta"

   Sun dauki tsayon lokaci haka, deeni duk ya fita ahaiyacin shi"

   Acikin wannan hali ummi ta riske su, babu abin da take ban da salati"

   Cikin sauri ma'u taja jikinta, deeni ko ya kasa sakinta sai kara binta yake yana rokota"

   Hannu ummi tasa ta rike ma'u, tare da fadin ke asma'u meya fito dake da tsohon daren nan"


    Ma'u bata iya cewa komai ba, kanta ta sunkuyar akasa"                     
   Kanta ta maida kan deeni daya rike hannun ma'u daya da kyau"

   Ta dade tana kallon cikin idon shi sannan tace, auta haka mukayi dakai"

    Jan ma'u ya fara, yana kokarin shiga dakinsa da ita, batare dayace wa ummi komai ba"

   Dan haka ummi tabi su, fadin take kai auta kana hauka be?, saketa mana"

    Ummi ina zuwa mana, akwai sakon da zan bata"

   Runtse ido tayi tana fadin bana so auta, kasake yariyan muta ne, ta wuce gida karka jawo mana abin mgn"

     Daramm gaban ma'u ya fadi, muryan Abba taji yana mata Yawo aka, lokacin da yake cewa.... da kijwo mana abin mgn gara namiki aure, cikin sauri ta zame hannunta ta fara kokarin tafiya"

   Binta deeni yayi ya sake jawo hannun ta, sannan ya matsa daf da ita, hannu yasa aljihu ya ciro wata yar karamar wuka acikin dan gidanta, ya mika mata, cikin rada yace ki rike wannan koda anyi nasaran kaiki gidan wannan danta shegiyan, inason ta zama filonki, ma'ana akarkashin filonki, kara cije baki yayi, ya dage shi sama, sannan yace, daya neme karban wani abu awajen ki, ki kaddamar mass"

   Kuma kisan yadda zakiyi kifito daga gidan tun kafin akiran asuba"

   Idan ban ganki ba zansan baki zamu daman fitowa bane, kuma washeri za'a daura miki aure, idan haka ta faru Asma'u, banason ki wuce kwana 3 banji lbrn mutuwan Jamal ba, idan kuma kin kasa kina da no zamuyi waya"

   Kuskus sukai mgnr dan haka babu mejinsu"

  Ummi ce tarako asma,u, tame cigaba da mata fadan ditowa da daddare"

 
 Tana isa kofar gidan ta cire takalminta ta rike ahannu, bakinta dauke da addu,ai"

   Allah ya tai make ta me gadin benan, hakane ya bata daman shiga gidan cikin sauki"

   Harta shiga bayi tai wanka ta fito tai sallah babu wadda ya nemeta"

    Dan haka tai zaune ta fara aikin nata wato kuka"

   Hayaniyan mutane taketaji cikin raha suna wasa da dariya, azuiyarta tace dafa haka kawai ne da yanzun ina cikin su ina kasan dariya"

   Zuwa can tafarajin ana cewa wai ina amaryan ne ya kamata asata alallai dare nayi"

    Cikin sauri ta juya ta haye gado ta kudunne kanta"

   Wata kanwar mama ce ta shigo ta yaye bargon ta fesheta da turare, sannan ta rangada guda"

   Ba ma'u kadai cikinta ya karta ba harda na jamal, jin wannan gud'a ya tabbatar mai auren nan babu fashi"

   Dare ya tsala kowa yayi shirin bacci amman banda ma'u, zau ne tayi ta rafka uban dagumi"

    Da misalin karfe 4:30am ta fara jin wani dan siririn fito, haka ya tabbatar mata deeni ne, dan haka tafara kokari meman yadda zatayi ta fice"

   Waigawa tayi ta kalli Anty fa'iza dake kwance akan gadonta, tare da yariyar kanwar mama Khadija, bacci su suke kashir ban, dan haka ta mike, daman hijjabin ta, na jikinta ahankali ta bude kofofin tayi waje, a harabaan gidan taji gabanta na faduwa dalilin tunawa datayi, ai get din kwado ake samishi yanzun yaya kenan?, dan dakatawa tayi, zuwa can Wata zuciyar tace mata maza kisan duk yadda zakiyi kibar gidan nan, idan ba haka ba gobe Aure za,amiki da jamal"

   Guiwanta taji ya kara kwari dan tana ganin duk duniya babu wadda yakaita  tsanan jamal"

    Karasawa tayi bakin get din, abin da yayi matukar bata mamaki, abude gidan yake, ahankali ta bude karamar kofan ta fita"

   Cikin Sauri deeni ya karasu ya riketa da duk hannun wanshi guda biyu ido ya zuba mata zuwa can yace muje ko?

   Jikinta taji yayi sanyi ko wani hali Abba da mama zasu shiga idan suka wayi gari basu ganta ba, amman kuma bazata iya tsayawa ba, haka kurum ahadata da Jamal, dan haka ta gyada masa kai, tafiya suka fara amman ma'u saitaji kaman anfito daga cikin gidan"

   Waigawa tayi ta kalli get din, bataga komai ba, saboda duhu, dan haka ta juya sukaci haba da tafiya"

   Sunyi kaman taku 5 sukaga andallare su da filan mota mai tsananin haske"

   Gaba dayan su suka juya, ganin Abba tsaye abun yayi matukar razanata ahankali ta zame kasa tare da daura hannuwan ta aka, tana fadi na shiga uku na"

 Deeni ko fadi yake tashi muje asma,u karki yadda suyi nasara akan mu bazan iya rayuwa babu ke ba, kinsa ni ina tsananin sonki"

 Karasuwa Abba yayi cikin tsananin tashin hankali yace"

   Asma'u tashi Ki bishi, ai bansan cewa ni ban isa dake ba sai yau, dan haka bazan hanaki Ki bishi ba, amman kisani idan kika Saka kafa kika wuce nan wajen  Allah ya isa takanina dake, sai yanzun nake dana sanin saka miki sunan mahaifiyata danayi, baki cancanci sunan nan ba"

   Deeni ne ya karkace baki shi sama sanan yace toh saika goge sunan, maza sa ruwa ka goge sunan sunan tsuhuwar taka"

   Zare ido ma'u tayi abba ko kokarin karasawa gaban deeni yake, saida yaje dafda shi sannan ya bigi karjin deeni tare da fadin zakamin rashin kunya ne ai daman na sani kai d'in fitsararre ne"

   Murmushi deeni yayi sannan ya kalli ma'u yace tashi muje"

    Kuje Abba ya fada yana nunawa ma'u hanya tare da fadin tarihi ne zai maimaita kan shi, kallon deeni yayi cikin ido, sannan ya cigaba da cewa haka ubanka yayi Wa uwarka"

   Dan zaro ido deeni yayi tare da zuba su akan abba"

   Dan haka Abba yace, eh kaje ka tambayi uwarka saratu, ta gaya maka yadda tayi ta zame ka"


    Runtse ido deeni yayi tare da dunkule hannuwa"

  Abba ko juyawa yayi ya nufi gida, yana kaiwa saitin motan yace"

   Jamal sakko ka rufemin gidana"

    Ganin haka yasa ma'u ta mike tabi bayan abba aguje yana Saka kafa acikin gidan tana saka tata, kafafuwan shi ta rike tana kuka take fadin Abba ka yafe min"

   Hannu Yasa ya begeta tare da fadin na tsane Ki asma'u kin siremi, kwata2 Allah yacire min ke azuciya ta, tashi ki bani guri bana son ganin ki"

     Yana mgnr ne hannun shi dafe da kirjin shi"

   Muryan Jamal taji yana cewa, yi hakuri abba, ka yafe mata"

   Jamal baka ganin inda take neman tozarta ni bataga darajata ba bare da tausaya min, duk irin adalcin dana mata arayuwa, wlh 'ya'ya mata fitina ne, sun azaftar dani"

   Cikin sanyin jiki Jamal yace abba hakuri zaka yi jarabawa ce"

   Juyawa Abba yayi ya shige gida batare da yace komai ba"

   Dan haka Jamal ya juya ya kalli ma'u yace"

   Ke kuma tashi kiban guri tunkafin na hadaki da bango"

   Bata bari ya rufe baki ba, tamiki da sauri ta shige gida".

         *****



Deeni tsayawa yayi kaman gunki, mgnr abba ce ke mishi yawo akai, *kaje ka tambayi uwarka saratu, ta gaya maka yadda tayi ta same ka*"

    Jijiyon kan shi ne suka fito rudu rudu, idon shi yayi jawur kaman gar washi, acikin wannan halin ya isa gida, lokacin anfara kiran assalatu"

    A kitchen yaji motsin ummi dan haka ya manne ajikin bango"

   Besan abun da zaiyi ba damuwan ta mishi yawa, zuwa can ummi ta fito dauke da butu ahannun ta"

   Ganin deeni tsaye jikin kofa yasa ta fadin  Auta menene haka? Karka yadda son asma'u yasa ka zama rago, dan naga yana shirin zauta ka"

   Ummi inason nasan yadda kikayi kika same ni"

   Dafa kirji ummi tayi tare da fadin kaman ya?, ban gane ba?

   Ummi inason nasani wanene ubana, kuma yaya akayi aka same ni?

   Ajiye butan ummi tayi, cikin faduwan gaba ta matsa daf dashi tace"

    Auta wani yace maka baka da baba ne?, ai kai kasan uban ka, ahannun shi ka taso"

   Kara kankance wa idon deeni yayi, tare da fadin ummi ki fadamin kawai, kar kice zaki boye min wani abu, nafara mugun tunani akan ki, mahaifin asma'u yace nazo na tambaye ki yadda kikayi kika same in"

   Innalillahi wa inna ilaihir raju'un, zamewa tayi ta zauna akasa duk da cewa garin akwai sanyi amman ummi zafi takeji"

   Idon ummi gulu2 tace auta tashi muyi sallan saina kaya maka"

    Bazanyi ba yaseeen, idan kikaga nabar nan nasan matsaya ta"

      Binshi da kallo ummi tayi, tare dajin nadaama irin wacce bata taba ji ba"

   Tana matsanancin kuka tace"

   Auta akwai kuskuren babban Dana  ai kata abaya"

    Nakasan ce ni daya iyayrna suka haifa, dan Haka na tashi cikin gata, duk da cewa iyayena bawani karfi garesu ba"

   Mahaifina yana kokarin bani tarbiya daidai gwargwado harnakai munzalin Aure"

   Dan haka yamin baiko da yakubu Dan kanin sa, ana saura wata 2 aurena da ya kubu, wani bakon matashin saurayi ya sauka agidan mu"

    Ina daki naji baba na ya shigo dashi yana cewa ummata ga boko nan munyi, matafiye ne, yana neman masauki daga garin baguma can wani kyauye kafin akai Niger"

   Da hannu 2 mahaifiyata ta karbe shi"

    Baya Wata 1 shakuwa me karfi ta shiga tsakani na dashi, har takai idan yakubu yazu banason zuwa wajen shi"

    Dan haka yakubu ya farajin haushin bashir"

    Dahaka soyya me karfi ta kama mu nida bashir wato mahaifin ka"

    Shirye shiryen baki naga anatayi agidan mu, dan kaha naje nasamu baba, nace mishi nifah yanzun bashir nake so"

Nuna min yayi baxai yuyo ba, dan yariga yaba yakubu ni, tun ina karama, sannan yakara da cewa ban da abinki saratu, shi bashir ina mukasan asalin shi, bako ne fah?

    Haka na dage nifa bashir nake so, har ana saura kwana 3 ban daina cewa inason bashir ba"

    Bashirma kullum kara huremin kunne yake tare damin wasu abubuwa wadda basu dace ba, ana jibi bikina mahaifina yazo ya samemu cikin irin wannan hali, ranshi ya baci sosai dan haka ya kori bashir"

   Nikuma yayi fushi dani"

    Da misalin karfe 8:00 na daren ranan maman yakubu ta shigo da gudu tace ga yakubu can duk an yanke shi"

    Dan haka duk suka bita aka barni ni kaidai agidan"

    Bayan fitan su babu dadewa bashir ya shigo arude hado kayan ki muje"

   Bayiwa bashir musuba na hada kayana nabi bashi"

 
  Wanan tafiya tawa ita ta haddasar da halin da mike ciki ayanzun"

    Natafi batare da sanin halin da iyena zasu shiga ba"

   Bayan mun isa garin baguma tun kafin mu isa gidan su bashir, nafara ganin al'dar su tasha babban da tamu, kusan kowa ka gani da makami ahannun shi, muna isa kofar gidan bashir yaja ya tsaya tare da kallo na, sannan yace"

   Idan muka shiga gida zance ke matata ce, dan haka duk irin tanbayan da za'a miki kar bari musaba baki"

   Bayan mun shiga gidan sun karbeni hannu biyu, koda suka tanbaye shi ni, cewa yayi matar sa ce ni"

   Daki aka bamu ni da bashir, cikin kankanin lokaci Akasamu cikin ka"😭

    Sai alokacin nafara tunanin halin da iyaye na suke ciki, amman bashir akulum lallashi na yake, tare da bani duk wani abu da nake so"

   Dan haka na acire Kowa azuciyata naci gaba da zama harna haife ka"

    Sosai Bashir da mahaifin sa suke nuna maka kyauna basu barin kowa ya dake ka, koda nikai nace"

   Tun kana dan shekara goma kakanka ke tafiya farauta dakai, bashir ko akulum cikin koya maka fada yake, dan haka na matsa asaka amakaranta, bayan ka fara zuwa makaranta saina kula bakason karatu ko kaje makarantar ma, daga ace kayi fada da wannan, sai ace kayi da wancan"

   Idan ankawo karanka gida kuwa, bashir dariya yake tare da cewa, shi yasan danshi jarumi ne, idan kuna iyawa kuje kurama ma dan Ku"

   Komai girman Mutun baya kada ka afada, idai da wuka ne saidai ayanke juna, akarshe kuma kaine me nasara"

     Duk abinda kayi daidai ne awajan bashir, nikaina bani da bakin mgn"

    Har zuwa lokacin da kacika shekara 25, lokacin ne duk ka addabi mutanen garin"

    Nasan yana nan a idon ka, baka manta ba, kuma alukacin ne aka nemin baban ka aka rasa, wanda hakan yayi sanadiyan dawowan mu nan"

    Kuka deeni Yake sosai, take yaji ya tsani ummi, yana kukan yake fadin gsky kuncuce ni Ashe duk abinda ya faru dani kune sila, ku kuka jefani cikin halin da nake ciki, Ashe shiyasa danaje daukan Asma'u mu gudu abbanta yace tarihi zai maimaita kanshi?

   Tuni idon ummi suka kankance saboda tsabar kuka, auta karka sake ka raba asma'u da gidan iyayenta, dan shine abun daya zama min babban kuskure arayuwa ta, naiwa iyayena laifi babba, lokacin dana dawo na neme gafaran su, akace min shekaran su 2 da rasuwa, sai filin gidan gashi kana gani, da hannuta take nunamai tsakar gidan da suke zaune aciki, tare da kara rushewa da kuka"

   Shima deeni kai ya hade da guiwa yayi kuka me isar Sa"

    Rawan sanyi ummi ta fara deeni na kallo amman saboda tsabar jin zafita daya ke, yaki kulata"

     Zuwacan ya miki tsaye ya daga kanshi kasama tare da karkace baki, dan ya riga ya zaman mai jiki, guri daya ya kurawa ido sannan yace"

  Na rantse da sarkin dake busan numfashi saina auri Asma'u, babu uban da zambarwa, inanan inakan bakata, ko ana muxuru ana shaho saita dawo gareni"

   
     ****


Ma'u ko sanda ta shiga gida samu tayi kowa yana tsaye duk suntashi, kallonta kowa keyi dan haka ta gane sunji abin da yake faruwa"

   Koda ta shiga daki babu wadda ya biyuta, har misalin 12 na rana tana kwance"

   Haniyan mutanen da taji ya kara yawa haka ya tabbatar mata zancen auren nanan babu fashi"

   Zuwa can ta farajin karan motoci, mikewa tayi ta kama labulen window ta leka"

  Manyan mutane taga suna futowa mahaifin Jamal kawai ta shaida"

  Komawa tayi ta zauna ta daura tagumi, zuwacan ta sakejin wasu motocin nashigowa tare da hayaniya"

   Agogo ta kallah 2:30pm arikice ta miki afili tace yanzun dan Allah har 2 tayi, nashiga uku na"

    Gaban window ta tafi ta leka, Sojoji ne gungu2 hannun su rike da manyan bindigogi, wurin yacika makil da jama'a daga can ta hango Jamal sanye cikin shadda fara karrr, atsakiyan abukan shi yake, kowanne  fuskan shi dauke da murmushi amman tashi kamar amai mutuwa"

   Bakin gadon ta koma ta zauna, zuwa can taji maruki na fadin Alhamdulillahi andaura auren *Jamaludeeni* da *Asma'u*

  Jitayi kaman ansoka mata kibiya akirji, hawaye taso matsowa Amman sunki zobuwa, gefen gadon ta koma ta makure"

   Zuwa can taji anbude kofar ahankali ta dago kanta, momyn yaya usman ce, hannuta rike da kaya, abakin gadon ta ajiye kayan, sannan ta shiga toilet, zuwa can ta fito tace to taso maza yamma nayi"

    Kaman za'a kamata haka take tafiya' bayan tayi wanka ta fito momy ta mika mata kayan ta sanya zuruf suka shige, saboda tsabar raman da tayi"

   Komawa tayi ta zauna, tana haki, gyale momy ta yafa mata sannan tace tashi muje ke kadai ake jira"

    Wayyo momy🙆🏼 wlh nagaji, waida zan dan huta ne"

    Me kika yi? Maza taso muje"

   Haka taitabin bayan Momy kaman me koyon tafiya, har suka isa falon Abba"

   Zaunar da ita tayi sanna itama ta zauna tace toh Alhaji ga Asma'u nakawota tayi sallama, tare da neman gafarar ka zamu rakata dakin mijinta"

    Dauke kai abba yayi can gefe sannan yace kuje kawai Amina"

    Mutumin dake gefesa ne yace a,a bazayi haka ba, ya kamata kace wani abu"

     Kwantawa Abba yayi ajikin kujera ya rufe ido, dan haka mutumin yajuya ya kalli Asma'u

Yace barin ara bakinsa naci masa albasa, Allah yasa kije asa'a kinji ko?, Allah ya miki Albarka"

  Kuma Dan  Allah kiyiwa mijinki biyayya, yi nayi bari na bari"

  Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yace"

   Da zan umarci wani da ya yi wa wani sujada, da na umarci mace tayima mujinta sujada"

    Manzon Allah ya kara cewa"

Baya halatta ga matar aure tayi azumi kuma mujinta bayayi, face sai da izininsa, ba tada ikon zartar da wani Abu sai da izinin sa"

   Haka yaita mata nasiha amman agurin ma'u shiga yake yana fita domin ku fadi take azuciyata, Allah ya kyauta nawa Jamal biyayya"

    Har akasata amota kuka take, tare da kankame karamar jakanta ahannu"

   Ahaka suka nufi Abuja, gabanta na dukan uku uku, tare da addu,a insha Allahu jibi iwar haka zata sake biyo wannan hanyan"

   *Abuja*

 Sun shigo karfe tara da rabi na dare kai tsaye gidan Jamal suka nufa"

  Agaban wani tankasheshen gida sukaga drive ya tsaya, gida ne me dan karan kyau get din aka bude musu dan haka drive yasaka hancin motan cikin gidan, tun acikin mayafi ma'u ta hango haske kaman rana, ahankali ta dan daga gyalen ta tana kallon Gidan, amma me? Wasu sojoji tahango sunfi 10 suna shawagi haraban agidan tare da manyan bindigogi, kuma da alma agidan suke, cikinta taji ya karta, cikin sauri ta rike momy tare da fadi Momy wadannan agidan suke?

   Kallo momy tabi gurin da ma'u take kallo dashi sannan tace"

    Eh masu gadi ne?

Innalillahi wa inna laihir raju,un nashiga uku na"

  Momy na kokarin lallashin ma'u wayarta tai kara, dauka tayi tasa akunneta batace komai ba ta cire wayar akunneta ta mikawa ma'u tanacewa ansa Jamal zaiyi mgn dake"







Heart Beat
*Mmn Yazeed*

💗💝💝💗
​*BUGUN ZUCIYA*​
   ( ​Heartbeat​)

                   💓💝💗
                        💗           

💓💝💗
​By​
     💗
    ​​*Fadeela Lamido*




*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*



   4⃣7⃣ to 5⃣0⃣





🐕🐕🐕



Amsa wayar tayi badan ranta yaso ba, daga cikin wayar taji muryan Jamal yana cewa"

    Kafin ki shiga gidana ki ajiye Duk wani iskanci naki, akofar gida, karki shigan min dashi gida, dan bazan dauki rashin kunyar ki ba,"

   Bejara mezata ce ba ya kashe wayar"

   Guntun tsaki ma'u taja sannan ta mikawa momy wayarta, sake gyara mata gyale Momy tayi, sannan taja hannunta suka shi cikin Gidan, tare da ayarin mutanen da sukazo dasu"

    Suna shiga falon tasa hannunta ta bude idonta, dan ita bataga dalilin daza'a rufe mata ido ba"

   Idonta kiri kiri take kallon gidan, eh Gidan ya had'u kuma anzuba kayan daya dace aciki, amman ita basu bane agabanta, Allah ya sani tana masifar son deeni"

  Haka nan taji damuwan ta ya ragu sosai, dan haka ta shiga cikin su Anty fa'iza da Khadija da suke hira adakin daya ke matsayin dakin baccin ma,u"

   Su uku ne kadai adakin, manya suna falo suna kallo, dan haka anty fa'iza tayi amfani da daman tana bata shawara"

    Asma'u kinga jamal yana da kirki sosai, dan Allah ki bishi sauda kafa, ku zauna lfy, kuma ki guje duk abinda baya so"

   Toh kawai asma'u take cewa, Ganin haka Anty fa'iza ta ciro wani littafi ajakarta ta mika mata"

  Ranan kusan kwanan zaune sukayi, sunsha fira ammam hirar tafi karkata tsakanin Anty da khadija"


   Washegari suka tashi da shirin komawa gida dan haka hankalin ma'u ya tashi "

   Damisalin karfe 2 na rana suka fito domin kai asma'u gida momyn Jamal, su kuma  su wuce gida"


      Motoci aka kawo wadatattu"

   Bayan sun isa a gaban momy suka ajeta"

    Momy da yau ne ganin ma'u nafarko, ta taso da sauri ta kamata, kan cinyan ta, tasata tare da leka fuskan ma'u"

   Masha Allah, ta fada afili, sannan taci gaba da cewa Allah ya zaunar daku lfy"

   Daga nan su Momy suka yi sallama suka fice da nufin daddare Jamal zai mayar da ma'u

  Tun da suka fita ma'u najikin momy tana kuka, Nafisa ko na zaune agefe fuskan ta dauke da dariya"

   Bakomai ke bata dariyan ba kuwa illa, tunawa da tayi yaya Jamal baya son ahau gadon sa, kuma yau gashi da mata"

Har gurin karfe Goma, ma'u na gidan Momy, tana jaran Jamal har bacci ya fara deeban ta"

    Ganin ma'u na bacci Momy ta shiga kiran jamal awaya yana dauka tace"

   Jamal kana ina ?

  Ina gida mana momy"

   Gida ? toh ina Asma'un ?


Cike da kwarin guiwa yace gata akusa dani"

 Mamaki ne, ya kama momy, juyawa tayi ta kalli inda ma'u ke kwance sannan ta maida hankalin ta cikin wayar tare da fadin, kaniyar ka Jamal, abinda zakayi kenan?

   Me kuma nayi momy?

 Takaici ne ya kama momy harta rasa abin cewa, zuwa can tace kazo yanzun nan inason ganin ka"

  Cikin kankanin lokaci ya iso kai tsaye dakin momy ya shiga"

  Yan mata guda 2 ya gani suna bacci dan haka ya bisu sa Ido,  ya shaida nafisa amman dayar ya kasa tantaceta"

    Damamaki yace momy wacce wacece ?

   Uwarka ce, waikai sai yaushe zakai hankali, kirikiri ince maka ina Asma'u kace min wai gata, bayan tun da 'yan uwata zasu tafi suka kawo ta, toh inason insan abin da kake nufi?

   Jikin shi asanyaye yace toh momy Allah ya huci zuciyar ki"

  Mikewa momy tayi tana kokarin fita adakin take fadin, gatanan ta riga tayi bacci, sai kasan yadda zakayi, ficewa tayi abinta"

    Bin bayan momy yayi da kallo sannan ya juya ya kalli inda ma'u ke kwance ahankali ya matsa gurin cikin siririyar muryan shi yace ke, *Husna*, Husna,  ganin ya kirata su biyu bata tashi ba, yasa ya tsaya yana tunanin yadda zaiyi"

    Zuwa can ya matsa kusa da nafisa, hannu yasa yadan dake kafanta nan danan ta mike, sannan yace zoki tasa min Husna"

   Da saurinta ta taso, tana tashin asma'u, tashi tayi ta zauna tana mutsutsu ke ido"

   Lallan hannunta yabi da kallo, har ya kasa dauke idon sa ahankali yace tashi muje"

  Kuka ma'u ta fara tare da fadin nidai aban ni anan dan Allah"

  Harga Allah tabashi tausayi amman saiya mika hannu yana fadin zo muje dare yayi fah"

    Ganin bata da niyar tashi, yasa ya fita, afalo ya samu Momy dan haka yace,

Momy taki zowa fah"

    Harara momy tamai sannan ta nufi dakin zuwa cen ta fito rike da ma'u, kuka take sosai momy na lallashin ta, kiyi hakuri kinji idan ankwana biyu zanzo, in duba ki, idan naga bakijin dadi zaman sai kudawo nan, bayan momy ta zaunar da asma'u amota ta juya ta kalli Jamal tace kaikuma kaji tsoron Allah"

  Suna isa gida ta bude motan da sauka, shima saukowa yayi, Amman sai taga ya nufi wani bangare daban, ido kawai ta zuba mai acikin zuciyanta tace yana nufin ni kadai zan kwana awancen part din"

   Ahakali ta fara takawa harta shiga ciki, agogo ta kalla taga karfe goma sha biyu"

    Tagume tayi, tare da tausayin kanta, karamar jakanta ta dauka ta Bude' ahakali ta jawo sarkan deeni, kura mata ido tayi, hawaye taji yana sakko mata na takaice, rungume sarkan tayi tare da tunani yau wane hali deeeni zai shi?

    Ahaka ma'u ta kwana rungume da sarkan deeeni lolaci2 tana sunbatar ta"

   Washegari kuwa ko kyalin Jamal bata ganin ba, haka ta kwashe sati biyu bataga Jamal ba" dan haka tunanin ta ya fara canjawa, gashi babu waya ahannuta bare ta kira deeni taji wani wani hali yake ciki"

   Kara ramewa tayi tai baki, tai zuro2 da ita, domin babu me matsa mata data ci abinci, sai dai intaji cikinta na kugi ta shiga kitchen ta girka"

      *****

Yauma kamar kullum tana zaune afalo taji ana kokarin bode kofar"

   Kofar tabi da kallo Jamal ta gani ya kara wani haske tare da murjewan fata"

     Zama yayi akujeran dake kallon tata, ya kura mata ido"

      Zuwa can yace *Husna* babu ko gaisuwa?

    Shiru tayi tana kallon gefe, domin idan taganshi jitake kama ta kashe shi"

   Husna ina mgn kin min shiru"

    Shirun dai ta sakeyi ganin haka ya mike tare da fadin haryanzun dai baki gama yin taushi ba"

Ganin yana shirin ficewa yasa ta mike tana binshi abaya"

   Ja yayi ya tsaya tare da fadin ina zaki?

  Cikin kuka tace ni wlh nagaji nagaji da zama anan"

   Idon ya zuba mata tare da jin tausayin ta axuciyan shi"

    Idon shi akan karjin ta yace, toh yanzun yaya za'ayi kenan"

    Sunkuyar da kai tayi tare da wasa da hannuta"

   Inajinki menene matsalan"

   Ni gaskiya bana son gidan nan"

    Shiru yayi ya zuba mata ido, zuwa can yace, zanso kiso gidan nan Husna, garama Ki cire kinsa azuciyar ki, dan ko zaki fita gidan nan toh bayanzun ba"

    Kara matso wasu hawayen tayi, dan haka Jamal ya tsinta kanshi da kasa tafiya"


Tsayawa yayi ya tsare ta da ido, harta tsargu da kallon da yake mata"

    Zuwa can yace Husna kukan me kike yi?

    Uffam batace ba, hawaye ne kawai ke zuba kaman anbude famfu"

   Ahankali ya sake kiran sunanta, dago jajayen idonta tayi ta kalle shi tare dajan majina"

  Inason ki gaya min abin da yake damun ki, banason yawan koke koke, ke kuma naga dabi'arki kenan, ki gayamin meke damun Ki,

kidauka da usman kike mgn, dan nida usman bamu da banbanci, na amince da aureki ne dan na gyara miki zama, bawai dan zan iya rayuwar Aure dake ba, danni kinmin kankanta, kina fara hankali zan sallame ki, dan haka ki natsu zaman ki agidan nan na wani dan lokaci ne"

    Har ga Allah taji dadin mgnr shi, dan haka tasa hannu ta fara share hawaye"

    Dariya taso ba Jamal amman sai ya dake tare da juyawa ya fice"

   Kan kujara ma'u ta koma ta zauna, tare da tunanin hanyar da zata billowa Jamal bataso ace har yanzun tana garin nan ba, kuma yanzu dataji kalaman Jamal tafara canza shawara, ayanzun deeni ne kawai zai iya nemo masu mafuta, dan haka ta fara neman inda zata samu waya"

 Acikin zuciyanta tace wannan wata irin rayuwa ce, duk abi antsane ni, kowa baya sona, idan ba deeni ba babu me nunamin kulawa"

    Haka ta wuni tana tunani tare da zubar da hawaye"

   Tunda Jamal ya fita be sake shigowa ba har washegari"

 Damisalin karfe tara, tana kwance adakinta taji ana sallama afalo"

Mikewa tayi, jiki babu kwari ta fito, Momy tagani ita da nafisa, dan haka ta fara murmushi batare datasa sanda ya fitoba"

    Cikin sauri momy ta taho ta rike Asma'u, tajata kan kujera tare da mannata ajikinta"

   Duku da kanta tayi saitin na ma'u, gani tayi hawaye na zobowa a idon ta, hannu tasa ta fara share mata, sannan ta dagota tace"

   Asma'u me yake faruwa?, wani abu na damunki ne?

   Kukane ya kwace ma asma'u harda shashsheka, dan haka jikin momy yayi sanyi, waya ta daga ta kira Jamal, cikin kankanin lokaci ya iso"

  Har lokacin asma'u kuka take, dan haka ya tsaya ya tsareta da ido"

    Momy ma kallo ta bishi dashi, sannan tace, Jamal me yasa kake haka, dan Allah ka duba yariyar nan sati 2 kawai ji inda ta dawo?

   Momy to ai itace taki kwantar da hankalinta, kulum bata da aiki sai kuka, ni nagaji da koke2 haushi ma take ban"

      Jamal da kaga tana kukan ka tambayeta abinda yake damunta?

   Ai ni bata min mgn"

   Shiru momy tayi zuwa can tace, Jamal haka ake aure?, dahar zaka kalli tsabar idona kacemin wai batamaka mgn"

  Jamal bece komai ba, shiru falon yayi nadan wani lokaci, zuwa can momy ta sake cewa"

   Toh shikenan tunda abi haka ne, zantafi da ita gida, ku zauna abangaran ka"

    Dago kai Jamal yayi tare da fadin, a'a momy, daddy ma yace haka, amman nacemai ni nafison na zauna anan"

    Aiko daddyn naka idan yaga yadda yariyar nan ta fige bazai yadda da zaman ku anan ba, domin alamu sun nuna baka kula da ita, dan wannan kukan da take yi inda kana kula da ita bazata yishi ba"

   Juyawa momy tayi, kalli nafisa sannan tace Nafisa hadu mata kayanta"

     Shiru Jamal yayi yana karabin ma'u da kallo, aranshi beson su koma gida dan kwai abubuwa da dama daya shirya"

   Ma'u na jikin momy har suka bar gidan"

  Bayan sun isa gida haka momy taitajan ma'u ajikinta harta fara sakin jikinta"

   Damisalin karfe 7:30 na dare ma'u ta samu daman karban wayan nafisa, tashi tayi ta shige toilet"

    Shigar da no deeni tayi, cikin kankanin kokaci ya dauka tare da fadin Asma'u ? meyasa zakimin haka?

   Ajiyan zuciya tayi sannan tace deeni ? Yaya akayi kasan nice?

   Ajikina naji, asma'u nashiga cikin wani hali, ina tsananin bukatan ki akusa dani, Asma'u bani da gata, bani da kowa saike, me kikeyi har yanzun baki dawo ba?

    Cikin kuka tace na kasa, deeni bansan yadda zanyi ba"

    Shima hawaye ya share sannan yace Allah yasa baki bari ya shanyemin Furata ba"

  Kukan ma'u karuwa yayi, cikin muryanta da ta kasa fita sabo da kuka tace"

  A'a naka ne kai kadai, Yaya Jamal be isa yashata ba, dan yafi karfin sa"

   Ajiyan zuciya ya sauke, sannan yace kin tabbata?

   Eh ta fada cike da karfin guiwa"

   Shiru sukayi na wani lokaci, zuwa can, yace  awacce uguwa kuke?

   Bansan sunan unguwan ba deeni, tunda nazo ko kofar gida ban fitaba, nan ta kwashe duk yadda sukayi da Jamal ta fadawa deeni"

   Shuru yayi, zuwa can yace, Asma'u karki yadda da duk abinda Jamal zaice miki, karya yake, yana sonki, wlh muna fuki ne, nafahimci sonki yake, tun lokacin dayazo har gida shi da mutanen sa suka tafi dani, yace ki natsu ne dan ya samu hanyar da zai cusa miki soyayyar shi, bawani rabuwa da zaiyi dake karya yake yi"

   Hawaye ma'u ta share sannan tace toh yanzun yaya za,ayi?

 Karki sake kimai biyayya, duk abin da kika lura baya so shi zakiyi, karkiji tsoron sa ko kadan, na kula dan zafin kai ne, inaga yin hakan zai tunzura shi ya sake ki, sannan kiyi kokari ki binciko min sunan unguwan, tare da no wayar Jamal"

   Amsawa tayi cike da kwarin guiwa, dahaka ta kashe wayar badan tagaji dajin muryan deeni ba"

   Wanke fuskanta tayi sannan ta fito, babuwa adakin dan haka ta nufi falo"

    Fuskan momy dauke da murmushi take kallon ma'u, cike da kulawa tace, daman yanzun zan sa Nafisa ta kiraki, dan mijiki ya shigo tun d'azun"

   Daramm taji gaban ta ya fadi, sabo da yadda momy takira Jamal da sunan mijinta"

   Kira Momy ta kwalawa Nafisa, bayan ta iso tace rakata part din jamal"

   Jitayi cikinta na kugi anya kuwa zata iya yin abin da deeni yace"

   Data tuna fuskan Jamal takejin gabanta ya fadi, gsky tana shakkar sa, dan fuskan shi babu wasa"

  Suna cikin tafiya, ma'u ta juya ta kalli nafisa tace"

   Nifisa tsoron yaya Jamal nake, ban son zuwa kusa dashi"

   Da sauri nafisa ta kalleta tare da fadin kema?

   Fuskan ma'u dauke da mamaki tace, au kema yana miki masifa"

   Baki nafisa ta kama, tare da fadin ke ai wlh yaya jamal mugun masiffe ne, masifa ta masa yawa amman ai ke kila bazai miki ba?

   Shiru kawai ma'u ta mata, dan taga sun isa bakin kofar, suna taba kofar sukajita abude, dan haka suka shiga bakin su dauke da sallama"

   Yana zaune akan kujera yana yin abin da ya saba wato karatun jarida"

   Matsawa Nafisa tayi tabawa ma'u hanya ta shige sannan ta juya tare da fadin saida safe"

   Ke zonan"

   Da sauri Nafisa ta juyo ta kalle shi"

   Me kuka zo yi?

Momy ce tace na rako Anty Asma'u"

  Ki rakota? tamin me?

Kaji yaya jamal din nan da wata mgn, nafisa ta fada azuciyanta, afili kuwa cewa tayi"

  Bansan me zata maka ba, nima momy ce tace na rakota"

   Kan shi ya maida kan jaridan, ganin haka nafisa ta fice"

   Ma'u kujera ta samu daga gefen shi ta zauna"

  Ko kallon inda take beyi ba, sun dauki tsayon lokaci ahaka"

   Zuwa can ya waigo ya kalleta a hankali yace"

    Husna inajin bacci, zanje na kwanta, ke a ina zaki kwanta?

  Haushi tambayan ya bata dan haka tace duk inda kace"

  Kallonta yayi sannan ya sake cewa,  OK toh ki kwanta afalo, akafin gobe agyara miki dakin ki, ni gadona kananan yara basa hawa, dana barmiki, yana mgnr ne yana tafiya"

  Innalillahi wa inna ilaihir raju'un ta fada tare da bin bayan shi da kallo"

   Haba tayaya zan kwana afalo bayan tunda uwata ta haifeni bantaba kwana afalo ba, wannan wanni irin wulakacin ne zaice wani wai na kwana afalo, aiko bako ne yazo aka barshi, ya kwana afalo an wulakanta shi"

   Tunanin da taitayi kenan har gurin 12 tana xaune, zuwa can ta mike ta nufi bishi, dan ita bazata iya bacci afalo ba, kofar da taga yabi, ta tura,   kofufi guda uku ta gani ajere, na farkon ta tura"

   Daki ne lafiyayya babu Kowa aciki, yana zuba uban kamshi"

 Ajiyan zuciya ta sauke sannan ta shiga, nan taga jirin akwatunan ta dasuka taho dasu dazon, watoh jamal saboda tsabar mugunta ya barni na kwana afalo, dayake beda imani ko tausayi na, bayaji"

   Washegari da safe ta fitoh da nufin zuwa part din momy"

   Ta kusa isa ta hango megadin gidan yana zaune da redio sa ahannu, azuciyarta tace"

  Barinje in tambaye shi, wacce unguwa muke, karasawa tayi tanayi tana wai wayen bayanta"

   Takusa isa taji muryan jamal, Ke Husna"

   Afirgice ta waigo tana kallon shi"

   Ina zaki ?

   Dawowa tayi da baya tana kokarin shga part din Momy, amman saitaji jamal yace karki shiga, wa kika tambaya kafin kiki fito?

    Ahankali ta dawo baya, tana zuwa daidai gurin shi, yasa hannu ya matse kunneta tare da fadin, ke wai wacce irin yariya ce? me kikaje yi kuma gurin me gadi? sai kace wata ballah gaza"

   Zafin da taji shi yasata ta fitar da Wata yar kara, tare da kama hannun nashi tana kokarin cirewa akunneta"

   Yarrrr yaji ajikin shi, sanadiyan kama mai hannu da tayi, nan danan jikin shi ya mace, daker ya iya bude baki yace"

   Kina ganin kaman zaki iya kwatan kanki ahannu nane?, ko wannan dan iskan saurayin naki idan na rikeshi bazai iya kwatan kashi ahannuna ba, bare ke, kuma bazan sake ki ba harsai kin gaya min me kikaje yi agurin"

   Saboda tsananin azaban da take ji batasan sanda tace, rake fah nake son sha, shine naje na bashi ya sayo min"

   Tirrrrr, rake? natsani naga mace nashan rake, amman nasan..... Kome ya tuna kuma sai yayi mormushi sannan yace, ina kudin ?

   Tsuro tsuro tayi ganin haka ya sake yin murmushi, sannan ya saki kunnen ta yace"

   OK, rake zakisha ko? barin naje na nemo miki"

   Juyawa yayi ya fita, zuwa can ya dawo ya mika mata ledan hannun shi, tare da fadin daga yanzun duk abin da kike so, kimin mgn zan kawo miki"

    Gefe ya koma ya zauna, duk da cewa bawai son raken take ba, amman da ta tuna yace beson yaga mace nashan rake, yasa ta dauko ta fara sha"

   Shiko jamal yadda ta daddage take shan raken abin yaso bashi dariya, hakanan yaji tana burge shi"

   Tas ta shanye raken, sannan ta mike tana kwashe bawon"

    Cikin shi cike da dariya yake satan kallonta, harta shige daki yana bin bayanta da kallo"

   11:41pm Jamal kwace akan gado, bacci yaki zuwa duk inda ya juya Husna yake gani lokacin da take shan rake, dariya yayi kadan, sannan ya dada gyara kwanciyan shi, ji yayi kaman gadon yamai fadi dan haka ya jawo folo ya rungu me


  Itako ma'u ganin Jamal be nuna fushin shi ba, yasa ta daukan alkawarin sashi yin fushi, dan haka ta tashi ta nufi dakin jamal"

  Kayan bacci ne ajikinta dan haka ta dauki hijjabi ta daura kai"

   Ahakali take buga kofan"

   Waye ? taji ya fada"

   Murya kasa kasa tace nice"

   Saukowa ya fara yi, tare da fadin menene ?

   Daidai lokacin daya bude kofar ya kura mata ido"

   Turu baki tayi kadan tare dayin kwalkwal da ido, sannan tace"
 
    Rake zan sha"






Heart Beat
*Mmn Yazeed*
adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *