Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, September 2, 2019

CIWON SO COMPLETE HAUSA NOVEL

adsense here
CIWON SO COMPLETE HAUSA NOVEL
[1/7, 7:36 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔



        Na
Hafsat ( Hafsy baby)

Da sunan Allah mai rahama mai jinkai.

1




Yan Mata guda biyu  sunata shiri zasu school  adauki  wannan A shafa wannan  cikin sauri  Meenat tadauko kaya tasa Amma safeeya  batada niyyar tashi A bakin mirror  har Meenat tasa cikin fada Meenat tace Amma kinsan yau  muda lecture din Dr Ahmed kuma shine first, kuma kinsan idan ya shiga  class babu wadda zai Kara shiga Amma  kintsaya sai wani lindar fuska kike.  Safiyya tace sorry, sis  yanzu Zan tashi  kikara hakuri. Tana idarwa  ta wuce ma' adanar  kayansu(wadrope) tasawani red din  material  Masha  Allah tayi kyau  Abinka da farar Mace  suka fito  suka iske  umma da Abba bisa dinning table domin break fast  suka hada baki morning umma, morning. Abba, umma da Abba suka ce lafiya twins din Umma da dady. Sukaja kujera  suka zauna sharp sharp sukayi break fast.  Suka mike umma nd Abba muntafi school.  Suka A dawo lfy. Suna. Fitowa  safeeya tace pls, my sis  kiyi driving zuwa school  banason bata kwalliya na. Meenat tace chabb!! Sai dai  muyi late sai inatukamu  cikin fuskar rarrshin safeeya  tace pls my sister nandai ta rarrsheta sukaje  ( ummaru musa yar aduwa university).bayan sun isa  suna shiga  Suka nufi class  suka zauna  ko 5 minutes baayi ba saiga Dr Ahmed.ya shigo  nanda    kowa ya shiga  hankalinsa   yan Mata kuwa kowace  jiki yace morning class. Sukace morning sir, yarubata test   bisa Allo  kowa ya firgita da hakan  30 mints yabada kowa yagama. Nan safeeya ta kalli  Meenat masu   niyya suka Fara masu maida hankali  Akan Abinda Ake  saffiya ta tambayi  wani question  tabata ganeba  Dr Ahmed  ya Lura  da itah  yace  ke get out, tace pls. Sir Am sorry  yace I say get out  cikin sanyi jiki ta tashi  tabar class din.
[1/7, 10:48 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔



Na


Hafsat ( Hafsy baby)

02

Safeeya  na fita ta nufi wani wajen da babu mutane sosaitazauna tayi tagumi  tafada tunani zuciyata meyasa kikayiman haka nafada cikin son Dr Ahmed  mutumin daya tsane ni bayason ganina ba batasan sadda hawaye ke tsiyaya da fuskar ta ba    saboda  CIWON SO Dr Ahmed kedamunta kullum kara yawa yake tare da itah. Kamshi wani turare taji mai kamshi ya ziyarci   A hanci  tadago  fuska ta ga waye sai sukayi Arba da Dr  Ahmed ya wuce da  barandar datake zaune. Can taji wasu  yan Mata na gulmar suna cewa keh Aseeya wallahi Dr Ahmed ya hadu Amma ya cika miskilanci. Rannan naje office din Amma kinga fuskar yadda kikasan bataba dariya haka yadaure  fuska  nayi sallama nashiga nace sir inayini cikin daure fuska ya Amsa yaceman meke tafe Dani  nacemasa Dama wutowa nazo yi nace bari nashigo bebari na ida ba ya kwasaman wata. Tsawa  yace nabarmishi office dinshi cikin sanyi jiki. Nafito nagayamiki. Safeeya taja wani tsaki tana takaicin wasu matan dake bada Kansu ga wasu mazan domin ita ko ciwon so zai kasheta bazata taba tarar dr Ahmed tace tana sonshi ba. Can kuwa bayan Meenat sun fito tana ta neman safeeya. Tarasa  can tagasu  wadda. Suke gaisawa. Ta tambyesu sunga safeeya suka ce tana baya can tanufa   ta iske ta zaune. Tace shine zaki bani wahala ko tace sorry sis Meenat ta nemi wuri ta zauna  tace wai sis mekika yima Dr Ahmed yake miki  haka ne safeeya  tace wallahi  sister bansan Abinda nayi masa yakeman haka. Tace yanzu yazakiyi da test din datawuceki tashi ne yau.  Kizo muje office dinsa mubashi hakuri  safeeya  tace. Sister kinsan hali Dr Ahmed bazai yiba tace  kedai   tazo muje. Cikin sanyi jiki ta tashi suka nufi Amma sai sukayi rashin sa' a office din kulle yake.
[1/8, 12:04 AM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔

Na

Hafsat (hafsy baby)

03
   Cikin damuwa Meenat tace kinga bayanan ko sis safeeya tace Eh mujuya gobe nashigo  dakaina da  munshigo school  din nabashi hakuri suka juya suka koma cikin makaranta  bayan sun idar da lecture din dasuke da itah suka hau mota suka nufi gida suna isa gida suka nufi dakinsu suka wasa ruwa Dama lokacin sallar Azahar yayi suka sallah Meenat ta Lura yau safeeya bata cikin walwala sosai  bata surutun nan Nata data Saba  tace wai sister meke damunki na Lura tun school bakya walwala meyafaru ne  ko tun abinda Dr Ahmed yayi miki  baki manta bane. Safeeya tace yazaayi na manta sis mutanan yatsaneni ban San Abinda nayimasa sister Abinka kadan ya  zan masa ya disgani cikin mutane kina kallo yau fa bani kadai nayi magana Amma nikadai ya hango yafiddo ni. Bata Ankara sai hawaye shar shar. A fuskarta domin wani ciwon so Dr Ahmed ke tasomata A zuciya  Meenat tace safeeya meyakai na kuka safeeya tace Abinda yakeman yasani kuka( batasan ciwon so Dr Ahmed  bane yasa safeeya (Hawaye.   Tace kiyi hakuri taso muje kinsan Umma batasan dawowar mu ba  suka nufi daki umma su  suka isketa zaune bisa darduma tana lazimi sukayi sallama suna shiga tagama laximin bayan ta idar tace yan biyun umma Andawo Eh, umma mundawo har munyi sallah ma tace toh madallah kuje  ga Abicin kucan bisa dinning koh. Sukace to umma suka nufi  dinning safeeya tura kawai take domin batasan  Meenat tafahimci halin datake ciki.  Bayan sun idar suka tashi suka nufi dakinsu.
Bayan sallar isha' I suna zaune falo da suna kallon labarai  da Abba su duka dai. Har wajen  karfe goma.  Sannan sukayi ma iyayen nasu sai da safe suka nufi dakinsu. Meenat naxuwa tafada gado  domin bacci takeji sosai. Safiyya tabi bayan ta Amma  takasa Bacci tunani Dr Ahmed kawai take sai juye juye take.har dai bacci yadauketa. Asuba tagari

Washe gari
Abba yashiga kwankwasa kofar su safeeya domin sallar Asuba domin kullum dayatashi sai yaxo   yatadasu  shikuma ya nufi masallachi. Bayan sun tashi sunyi sallah sai kuma su shiga kitchen domin shirya break fast domin umma batada yar Aiki bata bukatar ta  daga itah  sai yayanta. Bayan sun kamallah. Sukaje sukayi wanka  nanfa suka hau shirin school. Safeeya tajawo wata Arabia gown  tayi rolling da blue din gylen  Masha  Allah gaskiya tayi kyau domin sai da Meenat tace Kai sister kinga kyan dakikayi KO sai kace balarabiya. Safeeya tace Kai sister banason zolayafa tace Allah kuwa kin wanku. Nan suka yan Mata biyu kyawawa dasu suka gaida iyeyensu sukayi break suka nufi school cikin motarsu. Suna parking suka  fito  suka nufi class. Sungama daukar lecture ta farko sai kuma karfe 2:00 pm bayan sunfito. Safeeya tace sis bara naje office din Dr Ahmed naji yazamuyi dashi  game da test din jiya  Meenat tace muje tare mana safeeya tace A, a bara dai naje naje ni daya kinsan halinshi fa nan Meenat tace shikenan kije ki iske ni inda nadaki jiya . Safiyya tace OK , tajuya ta nufi office din Dr Ahmed cikin sa' a ta iskeshi bude gabanta na faduwa tayi sallama ta shiga.
[1/8, 12:08 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔

NA

hafsat ( Hafsy baby)

04
Safeeya nashiga  ta iske Dr Ahmed bisa table yana rubutu   tace sir Inayini  bai dago fuskar  yaga waye ba yace lafiya lau  yacigaba da rubutun sa  ta kusan 15 minutes tsaye sannnan yadago fuskar sa  cikin daure fuska yace meke tafe dakene. Nan kwarjinin sa yayima safeeya yawa domin ya tsare ta da manya idanuwansa. Tace sir hakuri nazo baka Akan test din dakayi jiya  kayi hakuri kasakeman wata. Yace sai dai kiyi hakuri kitari wata. Domin nawuce wannan Kuma. Kisake laifin haka nakara koranki. Ya sunkuyar dakanshi ya cigabada Abinda  yake. Cikin sanyi jiki safeeya  tafito ta nufi inda Meenat tace ta sameta can ta tanufa ta iske Meenat tana duba wani book.  Tace yane sis kindace tace A, a yace saidai natari wata kuma nakara Abinda nayi nakara  fita. Sister narasa abinda nayima  Dr Ahmed yatsaneni haka. Nan tafashe da kuka domin zuciyar ta wani zafi take Mata Meenat nace kiyi hakuri ki kyaleshi sister kinji ko nan ta rarrsheta. Lokacin  shiga lecture dinsu yayi suka tashi suka shiga. Bayan sunfito  suka nufi gida  Amma kowaya  san yau safeeya bata cikin walwala  daki tawuni yau.
Washe gari kamar yadda suka Saba sun isa school  suka nufi class Amma me suna shiga suka tarar da Dr Ahmed   ciki yafara lesson .  Amma yabada baya cikin sanda suka shiga  suka zauna  Joyowar  dai zaiyi saiyaga safeeya. Zaune yace keh!!!! Bakisan  dokokina ne ba fita kibarman class har Meenat ta mike zata bita yace kan yajuyo kwanta  yace badake nakeba ita kadai nake. Cikin fushi safeeya tatashi tafita cikin wani irin kuka mai ban tausayi  tafita  taji ma ta iya tsaya cikin school ba fitowa tayi ta tsaida nepep tanufi gida. Umma kawai ganni kawai tashigo tace lafiya safeeya kika dawo yanzu cikin dauriya tace umma bana lafiya ne  tace subhanallah!!! Meyasameki tace zazzabi ne tace jeki daki bari  nadauko miki magani safeeya tanufi dakinsu ta wurgar da mayafin da jakar tafada gado   ta kwanta bata jimaba  saiga umma da magani   takawomata tace maza  sha gabana nasan ki da kin magani. Nan tasha umma tace to Allah sawwaka tajuya tafita. Can kuma  Meenat tafito daga lecture Dama yau daya garesu. Taduba duk inda take tsammani  safeeya Amma bata Gantaba. Sai kawai takira wayanta. Safeeya tace tatafo gida.  Meenat kawai tashiga   mota tanufo gida. Ba. Inda tazame sai dakinsu ta iske safeeya kwance  tace  sis baki lafiya ne tace  inafitowa wani zazzabi ya rufeni kawai sai na tafo. Meenat tace har kinsa hankalina ya tashi wallahi. Meenat tace gaskiya Abinda Dr Ahmed yakemiki yayi yawa. Kodai ki manta Akwai Abinda yahadaku ne. Safeeya tace Wallahi sis babu Abinda  nayimasa.Tsane ce kawai. Amma  gobe bazan duba kwarjini dayakeman Zan tunkareshi naji menayimasa ya tsaneni haka.
[1/9, 12:07 AM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔


Na
Hafsat ( Hafsy baby)

 06
 

Wannan page din naki ne
    Nana A Usman  bisa kaunar book din nan dakike  Allah yabar kauna.



Meenat taja wani numfashi tace kinaga hakan zai yiyu kuwa sister safeeya tace hakan shine mafita sister   domin nagaji dahakan dayakeman kamar ni kadai  A fadi school. Meenat ta mike  tace ke bari naje dakin umma batasan nadawo ba domin nan kawai nayo domin hankalina yatashi wallahi. Daban ganki cikin school ba  tana shirin fita sai ga umma tashigo   tace Ahh,Ahh, yaushe kikadawo ne ke tace yanzu nashigo umma da Ina niyyar shiga   dakin ki sai gaki  kinshigo  umma tace nashigo ne dama naduba jikin  safeeya naga yajikin karfe Safeeya tace umma da sauki sosaima yanzu zantashi nayi  sallah ne. Umma tace to kitashi kiyi ga dan gidanki can nayi miki dan' wake  kiyi sallah sai kici  Nizan deka gidan  Kawunku   naji Alhaji nafadi dazu hajiya murja ta tazame da tayils ta goce da kafa  Anjima kinkara  jin sauki sai Ku leka kuganota. Safeeya tace sai kindawo umma.  Umma tajuya tafita.
Bayan sallar Magariba safeeya da Meenat suka nufi gidan kawunsu domin ga gida ga gida  suke suna shiga suka iske.  Haidar zai fita( dan kawunsu ne) haidar yace yafara washe hakora kamar me tallar close up,  safeeya takara daure fuska Meenat ce kawai tadan Saki fuska tace yaya haidar  Ina yini yace bazan Amsa ba Ku baa ganinku sai da dalili ko yanzu ma don mamy tagoce  dab aza gankuba ko Meenat tace wallahi karatu yadau zafi ne shi yasa . Haidr ya juya bangaren da safeeya take yace ke kurma ce  dabazakiyi ma mutane magana ba safeeya inayini bata jira ya Amsa ba tashigewar wata ciki  bata jira Meenat ba   Haidar ya kada Kai domin CIWON SO  Safeeya nadumshi tun lokacin da yafada Mata ta canza mishi. Bayan sun shiga ganin marar lafiya ne sun dan jima  suka fito suka nufi gida  bayan sallar Isha' ne suna zaune  A falo bayan sun gama cin Abinci dare  kamar yadda suka saba wajen karfe 10: 00 pm kowa ya nufi makwancin sa. Amma safeeya babu Abinda take sai juye juye bisa gado  domin wani fitanenen ciwon so Dr ke tasomata  kuma koda zai kasheta bazata iyah tunkarsa tace tana sonsa. Kuma gobe tayi Alkawarin tunkaranshi taji meta iyimishi ya tsaneta haka. Nan tana juye juye har bacci yasadodo ya saceta.Asuba ta gari yan  biyun umma.
[1/10, 12:14 AM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔
        Na
Hafsat ( Hafsy baby)


Jiya wajen rubata number 5 narubata number 6 sorry👏🏻👏🏻👏🏻


06

Washe. Gari kamar yadda suka saba  tashi suka gama Abinda suke suka nufi school. Suna fitowa safeeya tace zataje gun  Dr Ahmed. Meenat ta dakatar da itah tace tabari sufito daga lecture  sai taje office dinshi . Meenat suna  tafiya zuwa class take cewa nidama kin kyaleshi wallahi sister  duka kingi one year mu ida school din  fa, basai  yakara ganniki ba sannan zai miki. Nan gaban safeeya yafadi ta tuna kingi  shekara daya fa  su ida school  tadaina ganin muradin  ranta(Allah sarki So duk irinda Abinda yakemata bata gani zuciyarta taki fushi dashi)  Meenat tace sis yanaji kinyi shiru ne. Takakaro wani  nurmushi tace Ahhh,, babu komai sis  tunani nake wai kingi shekara daya mu ida  school. Daganan firar su tazo  karshe domin su iso class,   Bayan sun fito daga lecture ne   Meenat batasan zamewar safeeya tanufi office din Dr Ahmed.  Tana isa ta iske yana kokarin rufe. Office din  tayi sallama yajuyo yaga waye yanaga safeeya yace yakara daure fuska. Yacemata mekawoki wajena ba tunjiya mukayi magana dake ba  nakuma baki Amsa. Ya bita ta gabanta zai wuce. Safeeya tayi saurin shan gabanshi. Tace sir bawannan yakawoni  cikin fada  take magana yayi mamakin haka daga bakin safeeya  Amma benunamata ba yace  mekawoki  domin ina  da Abinyi Ina sauri ne nabaki  5 minutes kifadi Abinda yakawoki. Tace bazan wuce hakan ba domin banga Abin  tsayawa wajenka ( Karfin hali)
 Sir naga duk cikin school babu wadda katsana kamanta. Mekake takama dashi, Kudi, mulki, kyau,   komai daza kadinga wulakanta mutane yadda kakadama kasani babu Abinda  yakai mutum daraja Amma Kaine Abin wulakacika, Kullum duk Abinda kake takama dashi fa Akwai wadda yafika. Ina sanar dakai kabi duniya  A sannu  ba matabbbata. Ba wurine dazamaba nar har Abadaba. Wulakanta mutane kuma kacigaba. Banyi maka wannan Maganar daka daina tsanata ba Ahhh, na tunatar dakaine.  Nabarka lafiya. Safeeya tajuyo. Tatafi kawai  tabar Dr Ahmed tsaye kamar butun butun butumi domin tunda tafara Maganar ya kuramata Ido nan yaji wani Abu yanayimasa yawo  Akai ( tofa meye wannnan)    A bangaren safeeya  Kuma ba nufi wajen Meenat can baya takoma inda babu mutane tasha kukanta ta koshi har inda ta yacanza Allah sarki safeeya ciwon so Dr  Ahmed  na  Amma tadaure tayimasa magana. Haka .
[1/10, 6:04 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔
        Na
Hafsat ( Hafsy baby)


07

Safeeya nan wajen Tasha. Kuka tagaji taji kanta na ciwo. Tana niyyar mikewa taji wayanta na ringin taduba taga Meenat ce. Tace hello, Meenat cikin fada tace Ina kika shigane Ina nemakin tundazu  tace sorry sis ganinan zuwa. Bayan sun idar da lecture din suka nufi  gida. Kamar yadda bayan sun idar da Abinda suke sukayi ma iyayensu bakwana kowa yanufi makwancinsa   safeeya tafara tunanin datasaba kullum dare. Takasa bacci ma baki daya tatashi tayo Alwalla tayi sallah ra' ka biyu.  Ta roki  Allah yayemata son Dr Ahmed inba Alkairi bane. Tare da itah. Bayan tagama  tatashi tahau gado  ta kwanta can sama sama bacci  yafara daukar ta taji wani zafi  A kirjinta   tun tana daurewa har takai datafara numfashi sama sama. Can. Meenat taji kamar   A mafarki  taji numfashi  firgice tatashi ta kunna   lantarki taga safeeya ce cikin wannan halin   A firgice tace sister! Sister!!! Amma taga numfashinta sama sama kawai yake   A firgice ta Doro. Daga bisa Gado  ta nufi  Hanyar waje domin kiran Umma da Abba  tazuwa tashiga knocking din kyauren  Daki Abba. Da karfi A firgice umma da Abba suka farka  sukaji buga kyaure ba kaukautawa Abba yazo ya bude  kyauren  yaga Meenat yace meyafaru  Amina( domin haka yake kiranta) cikin kuka tafara magana Abba.. Safeeya bata lafiya gayanacan numfashi ta ....bebari ta ida yanufi dakinsu  da sauri    saidai umma tabi bayansa itada Meenat  suna shiga   suka iske safeeya tana ta numfashi sama- sama  da sauri Abba yace mikar da ita kafinan na fiddo mota cikin sauri Abba yafito don fiddo mota domin tafita Asibiti  yana fiddota su umma suka fiddo da safeeya tallabe baya Meenat suka shiga  Alheri clinic suka nufa domin can suke da file  suna isa suka fiddo da safeyya wadda takejin su sama sama. Suna shiga Akabata gado. Sunyi sa' a kuwa sun iske doctor dinsu wadda kedubasu. Nan danan yashiga duba Safeeya  yaga Abinda kedamunta yayi mamakin dayaga ciwon zuciya kedamunta har  yana nema yimata illah. Cikin zuciyarta. Yasan dai ba su rasa ci ba balle  kayan sawa tomeke damunta  ne nan yafito yacemusu  suje gida sai dasafe sudawo domin yanzu zasu ajeta dakin Hutu bata bukatar hayaniya  Abba yace doctor bazan barta ko yar uwata bace yace karku damu Alhaji daki dazamu ajeta bata bukatar kowa. Abba yace doctor jikin dai sauki yace da sauki mumata wasu Allurai yanzu. Tana bacci zuwa gobe insha Allah zata warware  Abba yace toh Allah yasan haka. Doctor yace  Ameen.






Abangaren Dr Ahmed kuwa tunda Safeeya tama gayamasa  magana  tajuya  tatafi   yakusan Minute 10 goma tsaye  yana tunanin  sannan yatuuka motar yabar makarantar  babu inda ya nufa sai gida yanashiga ya iske mahaifiyarshi  A falo  tana kallo  yayi sallama yace  Hajiya tace naa' m Babana meyafaru naga yanayinka ya canza ne. Yace babu komai tace Anya babana babu komai inbaka fadaman waza kafadamawa  ne yayi murmushi babu komai hajiya.  Yatashi zai shiga ciki tacemasa Ga Abincika can  kitchen naajemaka fa.  Yace yanzu dai bari nashiga ciki nayi wanka. Nadan kwanta  Ina fitowa zuwa Anjima naci  hajiya   taceshikenan sai kafito   yajuya ya shiga ciki hajiya tabisa da ido har yashige  ciki  tace nasan Akwai Abinda kedamun yaron zurfin cikinsa da miskilanci bazai Bari yafadaman ba tagirgiza Allah sawakka karya jama kansa wani ciwo Dr Ahmed nashiga babu inda yazarce sai dakin sa   yashiga toilet yawtsa ruwa yana fitowa  jallabiya kawai ya zura yahau gado domin yasamu bacci Amma inah  babu bacci magaganun Safeeya kemasa yawo.  Nan yafara tunanin  komai yacazama masa tsanar kowace mace cikin  Ranshi

Bayataba mancewa shekara 2 datawuce yadawo  daga  Kano yanacikin tafiya.....

KUBIYONI😝😛😜
[1/11, 5:00 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔
         Na
Hafsat ( Hafsy baby)
 

08


WAYE DR AHMED


DR Ahmed Dane ga  Alhaji Ibarahim kwangila   da hajiya Saudat.  Shi daya  Allah yabasu. Aràyuwa  yayi karatu   A kasar  Engalnd primary dinsa kawai yayi Akasar Nigeria. Yakai matakin har PHD  akasar Engaland   sunso rikeshi A kasar Amma yace kasarshi zaidawo Dr baya cikin wañaann shashan ya masu kudi wadda idan  Akatura  karatu sutai sharholiya.

Abokinsa daya  Hafiz. Shi kuma dan garin kano ne  shima Hafiz babu ruwansa karatu suka  sa gaba.  Babu ruwansu da shaye shaye ko neman Mata.suka dawo gida Nigeria  Dr Ahmed yasamu Aiki  A ummaru musa yar aduwa university.

Dr Ahmed zayakai 32 years fari dogo  ga hanci   gashi sumar sa  kamar kamar yanashafa Mata mai . Kai gaskiya Dr Ahmed ba karya ya hadu( dole saffeyya ta rude😃😃.

Maihifinsa yarasu shekara daya data wuce hanyar sa tadawo daga Abuja. Hajiya saudat taji mutuwar mijinta uba danta  domin Allah ne gatanta mijinta gata ta domin  yan garin    Rimin local government  ita dashi tatashi  A hannun kishiyar maihafiyarta domin wajen haihuwarta mahaifiyarta tarasu su ukku ita da yayyenta  yaya sule, yaya mustapa sai itah  kishirya maifiyarsu masiffatace Muguwa  domin fuska biyu gareta in maihaifinsu nan zata nunamsu Amma da yasa kafa yabar gidan  zata Fara dukansu har tagaji.Abinci ma bata basu sai in maihaifinanan. Daga baya ma saita Asirce maihaifin nasu ko gaban idonsa dukansu take.Abinci saitagama dabasu nan ta tilas tawa sai yakai yakai mustapha da  Sule karatun Allo tundai mahaifin nasu ya kaucewa domin yana son  yayanshi sharrin Ade ne kawai (Allah yaravamu da mugunta)

Har dai taci galaba kanshi  yakaisu garin katsina Karatun Allo. Daganan fa Hajiya  saudt( mahaifiyar Dr Ahmed) tazama baiwa komai na gidan itakeyinsa   Har takai Kimanin shekara17 samari sukayo Mata Ricah domin kyakyawa ce ga babu wadda tafidda ciki sai Iro. (Maihaifin dr Ahmed)   nan dai Akayi bikin babu abinda Aka kaimata sai tabarma da fillo da cooler kwara daya taso ayi bikinta yayayenta nan nan Amma tun lokacin da babansu yakoma malamin yace  tun   wanilokacin dasuka fita bara bai kara  ganinsuva. Maihaifin so yadawo hankalinshi tashe. Yana fadima Ade Amma data murza kambu Asiri sai yabar maganarsu.
Ayin bikin saudat babu dangi maihaifiya.   Domin tun lokacin  DA. Mahaifyar su saudat tarasu   sukaso su tafi dash Amma maifinsu yahana sukayi fushi suka tafiyar su basu kar waiwayensuba. Haka Akayi bikinta  Bayan wata daya  bikin Iro yaje cikin katsina yagamu da Abokinsa wadda sukayi karatu yasamu Aiki daganan har yayimasa hanya yasamu Aiki.daganan yakoma Alhaji ibarhim kwangila. Anabashi kwangilar makaratu  masallachi,   rijiyoyi. Kumabaya  ha inchi cikin Aikinsa  shiyasa  yayi Suna . daganan sukadawo cikin katsina  suka gyara gidansu na rimi saidai insu dawo su sauka ciki dawowarsu da katsina shekara daya Aka haifi Dr Ahmed.

Abin yasamo Asali dalilin dayasa Dr Ahmed yatsani mace.  Wata rana yadawo daga kano wajen Amininsa  Dr Hafiz  yakaimasa ziyara yazo daidai welcome to katsina saiyaga mace tsaye da hijabi tana daga hannu   beyi niyyar tsayawaba  Amma wata zuciyar  tasa yayo baya  cikin sauri tazo gabanshi ta tsaya yace  cikin fuskar damuwa tace ya taimaka Mata mahaifiyar tace Asibiti bata lafiya.  Yamikata gashi kuma bata da kudin zuwa . nan ya tausayamata domin ko yanayi shigarta  zaka  San  tana cikin  talauchi.
[1/11, 8:29 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔
           Na
Hafsat (Hafsy baby)

09

Dr Ahmed yace shigo tanashiga sunfara  tafiya yace wane hospital ne , tacemasa General hospital,  yace OK, sun isa General. Yakaita har can ciki  tafito tace masa nagode. Yace babu damuwa yafito yace mushiga  naga marar lafiya . domin nasamu Lada ko tayi murmushi  tace nagode. Sunashiga cikin haske Dr Ahmed yaga wannan budurwa kyakyawace Amma   talauchi yamaidata wata kalah.

Sun isa dakin da Aka kwantar da marar lafiya  Dr duk yayi ma majinyyata sannu har suka isa gadon  da wannan tanufa  tanazuwa tazuwa ta tambayi wani. Yaro dabazai wuce 14 years ba Khalipa yajikin Inna ne  khalipa wadda ta tambaya  yace gayanan tunda kikabarta tana bacci haryanxu shi take  yi kinsamo Kudin maganin domin tafiyarki Doctor yashigo sai fada yake Akan rashi sayen magani Kan lokacin.

Dr Ahmed yaji tausayi yaratsa masa zuciya  yayi gyaran murya  yace muga takardar magani kalipa yace Yaya Basma wannann waye.  Tace shine naroki Alfaarma yarageman hanya Akan dawowata daga gidan Kawu Yusuf.  Dr Ahmed ya Amshi takardar daga hannun basma wadda yaji sunanta bakin  Kanneta   yanufi pharmacy din cikin Asibiti yasiyo magagunan duk daaka rubuta  yakawomusu    yace su Kira likita sai ya gwadamusu  yadda zasuyi Amfani dasu yace saidayaga komai ya kammalla. Yajuya zaitafi  Basma tabishi daga baya.

 Tace nagode Allah saka da Alkairi  bawan Allah daban samu wannnan daga gareka Daban san yadda Zanyi yau ba. Dr Ahmed yace babu damuwa har sukaxo wajen motarshi zai shiga tace kabani number ka  koma ringa gaisawa ko.  Gashi zakatafi bansan sunankaba.   Yace sunana Ahmed
Tace wow nyc name, nan yakaaranto masa number wayansa tasa. Yajuya yanufi hanyar gidan su dake Kwado.
Basma kuma tayi murmushi tace cikin ranta  burina yakusa cika Zan Auri mai  mota.Kuma kyakyawa  (Tofaa daganin sarkin fawa)


One week later


Dr Ahmed ne  zaune yana duba wasu papers,  yaji wayansa naringi yana dubawa yaga new number ne  Kamar bazai dauka Amma kawai yadauka yayi shiru can  Akace hello yaji murya mace hello wake magana.  Akacemasa  Basma ce  yace Basma wace vasma dominshi har ga Allah yamanta da bayaninta cikin ranshi tace Wadda kataimakawa rannnan  nan tayimasa bayani  yace Ayya!! Sorry nagane  ykk yamaijiki tace dasauki har An sallememuma.  Yau kwana Ukku Inna natayimaka godiya nancema tayi nakiraka  kayiman kwantacen gidanku zatazoyi maka godiya. Dr Ahmed  yace kicemata na hutar da ita  basai tazoba  saidai kibani Address naku inasamu time zanshgo  ganinanta wani dadi yaratsa Basma (Tofah🙄🙄)
Nan tayimasa kwantacen gidansu Unguwar Yammawa.
[1/12, 8:18 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔
         Na
Hafsat( Hafsy baby)

Wannnan page naki ne . nasadaukar dashi gareki. Aunty Saheeba Lagos.

10



Basma tana datse wayar ta waiwayen wajen wadda suke zaune tace burina yakusa. Cika munerrat  wadda aka Kira da munerrat tace shakaman meyafaru Kawata  Basma tace kinsa yau ko sati biyu baayi da kwanciyar umma Asibiti ba  nan tafada yadda suka hadu Dr Ahmed.  Kuma   kinsa wani Abu Kawata wallahi  yahadu daganinashi Akwai Kudi.  Shiyasa Zan likemashi Har sai nasamu soyayar  shi. Munerrat tace nadauka wannan burin yafita daga ranki  nabaki Auren talaka sai mai Kudi  Basma tace chabb!!! Inanh burina nanan na wayagayamiki Auren  soyaya Zanyi Ai ingayimiki Ko yanzu nasamu wadda yafi Ahmed wallahi komin tsufanshi Zan Aureshi nataso cikin talaushi Kuma na Auri  dan uwana talaka. Munerrat  tace shegiya Kawata kina wuta,  tace kedai bari. Dai muga zuwa Ahmed din.
****************************
****************************

Abangaren Dr Ahmed kuwa saida sukayi kwana biyu da waya da basma sannan yazo Gidansu Dayazo saiyakira wayanta wadda yayi saving da help, tafito tayimasa iso wajen innata  tashiga dashi aga ibo masa ruwa. Cikin kwano duk lamba yanakaiwa yaji wani karni Amma hakanan yadaure yayi mashi kurba daya don karsu gane hakan.

Inna tayimasa  Godiya kamar me  nan yamike nan yana mikewa yazaro bandir   yan 200 ya ajemata  yace gashi  nan. Inna kamar tayi Kuka taitayimasa godiya. Yafito waje  Basma  tabiyo bayansa Yaya Ahmed Angode Allah saka da Alkairi tana ta fari da idanuwa  tasa wata Atamfa yellow da red. Wadda ta Aro wajen  kawarta munerrat. Yace babu damuwa yashiga mota yabar unguwa.

Daganan tun lokacin Basma tashiga isar Dr Ahmed da waya tun bai kulata   yana shareta  har yana  har yakai yana daga wayanta.  Daganan fa  soyayya tashiga tsakanin Dr Ahmed da basma. Domin basma tana da kyau ba laifi.


Daganan  Dr Ahmed yaga halin dasuke cike yagyara musu gidan  dasuke   ciki, yashiga dinka Basma sutura Kala Kala masu tsada   Daganan Basma tashiga wani girman Kai, tadinga jinta Kamar diyar shugaban Kasa, bata iyi ma yan unguwar su magana.   Bata harka da sai da yayayen masu Kudi,

*********************************†**************†*******

Soyaya tayi  Nisa tsakanin Dr Ahmed da Basma   fa babu Kama Hannun yaro. Har yana niyyar fada ba. Daddy dinsa Akan Aiko Gidan su Basma domin ayi Maganar Maganar Manya kwatsam!!! Rannan Basma taje bikin wata kawarta   diyar masu Hannu da shuni( domin Basma tacika  shige shige inhar yayan masu shine)

KOBIYONI.ZAKUJI KOMAI
[1/13, 4:24 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔
        Na
Hafsat ( Hafsy baby)



11



Basma Anje bikin kawarta Anata yatsina saikace  batasan wani Abu talauchi ba.
Anharde bisa Kujera Anata latsa wayar Tecno C8 wadda ko sati daya batayi ba Dr Ahmed yasiyamata  itah.   Saitaji sallama bisa Kanta  tadago Kanta ta Amsa ciki ciki yace ko gimbiyar Mata zata bani damar zama. Tadago fuska tasake kalleshi taga bakalar talaka bane( kuji Basma da karfin hali😊😊)

Tace babu damuwa zauna yajawo Kujera Kusa da itah yazauna yacemata  Barka da dare tace yauwa yace da farko sunana  Mahmoud  Kabir Nakowa. Basma tadago fuskarta A razane koshi yalura dahakan yace Kina mamaki ne Ko  tace wadda nakeji A gari bama A gariba duka Nigeria Kowa yasan shi  yace  Shikam. Basma ta jinjina Cikin Ranta  ( LaiLai)

Yace tunda kikashigo wurinan naketa hangeki Kuma naga kinyi mini Inasonki  Kozan samu karbuwa wajenki Kuwa???  Basma tayi Murmurshi tace Hmmm.

Mahmud bai wurinba saida suka Kulla soyaya da Basma  ya Amshi phone number ta tabashi Address din gidansu Ataikacedai shiyamaidata gida. Da akatashi daga party.

**********************************************************************************


Daganan fa Komai yacanza tsaninta da  Dr Ahmed ta fara canza mishi inyakirata  saitaga dama tayi picking yace Mata meyasa hakanan sai tace bata Kusa da wayar(kuma kunsan wani Abu duk tarrayar da Dr Ahmed betaba fadamaata wayeshi ba).

Rannan  Dr Ahmed yazo Suna tsaye Basma wayanta sai ringin yake Amma taki dauka. Dr Ahmed yace Mata waye ke kiranki ne kinki dauka tundazu. Tace wata friend dina plashing danazo Dauka zata Katse ne. OK  suka cigaba da zance   Amma Abu takama waige  waige dahaka sukayi dai bakwana yatafi yazo fitowa yaga wata mota itama tashigo Kuma bangaren Gidan su Basma tanufa Amma bekawo ma ranshi komai ba yatafi.

************************************************************************************

Kwatsam!!!!! Rannnnan Dr Ahmed bai Sanar da Basma zai zoba kawai yazo  yanazuwa. Kofar gidansu yaga motar dayagani rannnan nan yakira wayar Basma saidayayi Mata Kira 3 Kawai yaga Basma tafito daga cikin wannan motar tana dariya. Naciki Kuma yaja yabar wurin jiyowar da Basma zatayi kawai taga Dr  Ahmed ta firgita dagannishi Amma kawai tabasar tanufo wurinshi tace yallabai shine ko A sanardani zakazo ne. Yace kawai wurinki naji Ina shaawar zuwa ne.Basma Ina. Wayar ki nayi miki Kira Ukku bakiyi picking ba  Kuma waye yazo wajenki yanzu  questions 2 yajero mata duk tare sorry my dear wayana silance take banji Kirankabane. Wannnan Kuma wadda kaganni saurayin munerrat ne yakawo kararta Akan Abinda takemasa ne. Nan dai ta Dr Ahmed yadaina Zancen. Suka cigaba da firar har lokacin tafiyarshi yayi yatafi.

Lokaci natafiya kwanaki Suna Kara Yawa.Basma ce zaune. Ita da kawarta  munerrat  A dakin  Basma wadda  yasha yagyara. Munnert kecewa basma  Yanzu ki kyauta Kina tarrayya da Ahmed  Kuma Bikin da  Mahmoud kingi  1 weeks. Bazaki Sanardashiba Gaskiya bazaki Aureshi ba??

Basma taya tsina Fuska tace  dama Ai bamuyi yarjeniyaya dashi zau Aureshi  ba  ga ida Zan huta. Na hau motar danake so. Saina tsaya ma mai mota daya( 😊Rashin Sani) kyauttata da Ahmed bata wuce 10k zuwa 20k. Iyakarta takenan kiduba Mahmud Ko  A sandiyar kyautar dayakkeman  nabude Account yanzu Haka Ina  2 million ciki. Inbaki mantaba nafadamiki bazan taba Aure soyaya ba Aure Kudi Zanyi. Ahmed Kuma dama  nafadamasa mun tafiya  kauyen su Baba  kawai sai dai yaji Sanarwa. Suka kwashe da dariya. Munerrat  tace Amma baki kyautaba Kawata. Basma tace  Kinga tashi mushiga  Kasuwa Akwai Abinda  nakeson siya.

  *****************************************"**************   Bayan Sati daya


Dr Ahmed zaune dakinsa yanajin labarai yanata trying din number Basma  taki shiga domin yanason yasanar da itah cikin sati nan zai turo iyeyensa ( nufinshi inya fadamata gobe sai yasanar da daddy)

Anagama labarai kawai yaga Anhasko  wani hall da Da mutane ciki anata cashewa can aka hasko fuskar Amarya DA  Ango yaga kamar yasan fuskar Amarya Kamar sunsa Abinda ke ranshi  Aka Kara dallaro fuskar zata ba Angonta Cake A baki. Kawai yaga fuskar Basma  ya mike razane  yace karya ne Ba Basma danasi bace Basma bazata yaudareniba. Kawai yaji Ana wakar Bikin Amarya Basma da Angonta Mahmud sunyi Aure. Dr Ahmed yazauna ragwab!!! Bisa Gado  yace  Basma nizatayi makahaka nixata yaudara Amma bata  tabs nunaman ko Afuska ba .Amma babu komai Kanta ta cuta



Basai lokacin daya dauka yana  tunanin ba shigowar text  yaji  awayashi shine   yadauka yaduba yaga Basma ce. Tarutabamashi kamar haka



Aslm Ahmed dftn kana lafiya. Bawannan ba nasonka mutum  ne  mai Kallon  labarai  A kodayaushe. Kuma nasan zakaga wani Abu. Yabaka mamaki. Ba Abun mamakibane  Domin ba muyi  yarjejeniya dakai Zan Aureka. Inkuma   Kana  bukatar kudinka   tundaga wadda kabiyama   Inna Asibiti harzuwa yanzu zaka iya  zuwa  office din mijina  Mahmud kabir  Na kowa zaa biyaka bye bye.


Dr Ahmed yaja numfashi yagoge text din da number Basma baki daya
Daganan fa Dr Ahmed yatsani kowacce mace  Aranshi Domin tunanishi  duk haka suke( Anya kuwa)

Tofa shine Safeeya tafada ciwon so Dr Ahmed. Zata  cimmma burinta kuwa. Kuwa .???

Wane hali take yanzu A Asibiti ???

KUBIYONI...........
[1/14, 11:33 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔
          Na

Hafsat ( Hafsy baby)

12




A bangaren  Safeeya can kuwa wajen 12 Am tafarka daga Allura bacci da akayimata.

Taga babu kowa A dakin sai ita daya cikin ranta tace nasan su umma suka kawoni Asibiti to Ina sukaje.

Tanacikin wannnan tunane taji  Antoro kofa ta waiwaiya taga waye.
 Taga  Doctor  Sadeeq ne Family doctor dinsu ne.

Yazo har inda take yajawo kujerar yazauna yace Safeeya kinfarka ne,
Tace nafarka Doctor Sadeeq yace yanzu yakeke jin jikin naki ne  tace naji sauki.

Yace to Alhmdlh  safeeya. Yacemata safeeya meke damunki   ne Har ciwon zuciya yakamaki Haka irin wannan ciwon ne.
Dayayi yawa zuciya ke bugawa. Meke damunki haka gashi kinsa damuwa cikin ranki.

saffeya  tadukar dakanta kasa sai Hawaye cikin ranta tace Doctor Ciwon So mutumin dabasai  inayiba sai tsanata dayakema.

Amma bazan iya fadama kowan haka  tadago fuskarta tace Doctor kayi Hakuri bazaka iya jin komai bakina ba Amma Zan rage sa Abin cikin zuciyata insha Allah.


Dr Saddeq yace dayafiyi ko kima komai ga Allahh.kinji KO. Tace insha Allah. Yajuya zai fita Saffeyya tace Doctor Ina su umma ne???

Yace nace suje gidanane  domin baa bukatar kowa wajenki  sai gobe zasu dawo ne nima  inaga jikin yayi sauki  gobe Zan  baki sallama.

Haryajuya zai fita saffeya  tace    Amma... Doctor yace yane saffeya   yajuyo yadawo tace don Allah kada ka sanar da su Abba cewa ciwon zuciya ne.

Yace Mata meyasa tace masa don Allah kada kasanardasu Hakanan.
Kacemasu ulcer ne  ulcer ne.

Doctor yazare Ido😳😳 yace meyasa saffeya tace nidai Alfarma narokeka.tana niyyar Kuka☹☹

Yace tonaji Amma da sharadi?? Tace wane yace komai zaki cireshi cikin ranki . kidaina damun kanki. Inko baki dainanaba  zanfadama Abbanki Abinda kedamunki.

Tace insha Allah Zan cireshi doctor. Yace yauwa safeeya. Yanzu saiki kwanta kicire komai.  Cikin ranki kinjiko. Ta gydamasa Kai ya juya yafita.

  Saffeya  ta rintse idanuwanta wasu zafafen hawaye suka zubomata.

Cikin ranta tace Ya Allah ka cireman Dr Ahmed cikin raina inba Alkairi ne ba. A tare Dani. Domin wani sonshi  yaji yana Kara shiga Ranta. (Allah sarki saffeyya)


WASHE GARI



Abba da umma harda Meenat domin tace bazata school saffeyya bata lafiya.  ( yar Uwa  Rabin jiki)
 Suna shiga suka nufi office din Doctor suka iskeshi zaune A bisa kujera yana duba wasu file. Doctor saddeq yace Ahhh,,, Alhaji sannu dazuwa nan suka gaisa Abba yace doctor yajikin safeeya  ne yace  Alhmdlh zaku iya  zuwa  kuganta taji sauki yauma dasafe mun maidota dakin dakowa zai ganta.


Abba yace Alhmdlh to  Doctor yace muje nagwadamuku dakin suka rankaya suka nufi har dakin  suka iske safeeya kwance Meenat ta matsa wajenta sister yajikin safeeya tace mata dasauki saikawai taga Ashe tare suke dasu Umma tana kokarin mikewa ne Abba Aaaaa Safeeya kwanciyarki. Tace Abba da umma. Ina kwanku, suka ce mata lafiya lau Safeeya yajikin tace Alhmdlh. Sukace to Allah yakara sauki. Tace Ameen.Doctor yace Alhaji inkagama inason ganinka office. Abba yace to babu damuwa, Doctor yajuya yafita. Gaban saffeya yafadi.

Amma bata nunaba Abba yace bara naje umma tacemasa to.
Umma tace saffeyya kina iyawa Meenat takaraki toilet kiyi brush ko ruwan tea ne kisha, tace Eh Meenat takama ta suka shiga toilet.
Tadawo umma tahadamata tea mai kauri tana Kurba kadan kadan
Saiga Abba ya shigo cikin Fushi Gaban safeeya yafadi
Yace Safeeya mekika rasaAmmm....


KOBIYONI😘😘😘😘😘.        For comment

08164042255
[1/15, 3:49 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON  SO💔
        Na

Hafsat ( Hafsy baby)

13





Abba yashigo cikin fushi yace Safeeya meke damunki ne,haka, cikin inda zata Fara magana.

Umma tace Abba Yan  biyu me Doctor Din yafadamaka ne.

Yace man Ulcer ce takamata. Saboda rashin cin Abicin datake.  Mekikarasa rasa ne??  Ko meke damunki ne??

Safeeya tayi wata Ajiyar zuciya jin doctor befadi  Abba Abinda kedamunta.
Tadukar dakanta.

Batace dai komaiba. Abba yace Abinci kan yakare na aje wani.  A store.  Amma kifadi meye damuwarki.

Dahar yahanaki cin Abinchi ne?? Safeeya ta gigirza Kai Abba babu Abinda ke  damuna.

 Yace Kuma Har ulcer takamaki haka. Ne. Banason haka kinji ko kidinga cin Abinci.

Tace Abba zandiga ci insha Allah  yace yauwa yanzu inki gama ci  farfesu Rago zakici Ko Faten   doya zakici ne. Ta shagwabe fuska.

Abba sai zuwa Anjima  Anjima naci yace A,a kidaure kici inki gama shan tea din

 Safeeya tace Allah zanci Abba yanzu nacika cikina bakajiba.



Yace to shikennan Allah yakaimu Anjima to. Yanzu. Zan bar umma ki Zan tafi office sai nadawo. Allah sawwaka  tace. ameen  Abba.  Sai kadawo umma da Meenat sukace Allah yakiyaye yace Ameen  yajuya yafita.

Nan Safeeya tagama shan tea din suka dan tafa fira can  wajen  2 hour umma tace meza Samata takaradashi .


Tace Asamata  Fate doya yaji   wake da Alllayahu sai tashi Kamshi yake.
Can nahango  Aunty Saheeba itada Nana A Usman Suna   maida yawu Amma Safeeya taki yan  musu😉😉


Nandai Safeeya taci Harda tirsawawa umma taci da dan yawa. Ta Aje Tasha Magani da Doctor yakawomata dakanshi  yace shine zata sha insha Allah zataji sauki.

SCHOOL

Abangaren Dr Ahmed kuwa yau yashiga  school. Yanufi class dinsu Safeeya. Kawai sai nahango Dr Ahmed yana mika wuya yana waige waige ( Tofa meyake nema ne meya ke nema  kudai muje xuwa)


Yagama  Abinda yake yafita  babu Abinda  yanufa sai office dinshi yana zuwa ya zauna bisa kujera. Yadafe kanshi yace  meke damuna kardai Ace son wannan yarinya nake. Nan yafara tunanin domin  wata Rana   yashigo  school yaga Safeeya da Meenat    tundaga rannar Meenat tafara burgeshi saboda kamun kanta Amma yadinga karya ta zuciyar sa domin yace mace ba abin yarda bace. Daganan yafara  gwada Mata tsana domin  karyayi wasa sonta yashiga ranshi.

To Abin yakara rikicemasa tunda ga Ranar da  tazo har wurinshi.

Yau Kuma yashiga class dinsu begantaba ko tayi Fushi zata daina zuwa ne

 Akan Abinda nakemata.








For comment

08164042255.
[1/16, 6:52 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔
            Na

Hafsat ( Hafsy baby)

14

 Kuyi hakuri masoyan Ciwon so jiya nayi mistake wajen Rubuta sunan   saffeya. Inda Dr Ahmed ketunani sai Na rubuta sunan Meenat kuyiman Afuwa👏🏻👏🏻


Asibiti.


Doctor ne ya shigo dakin da Safeeya take  yatadda ita daya su umma taje  gida  tadawo domin girkin Rana,

Meenat Kuma  tadan fita  tadawo, Doctor yace safeeya yakike jikin yanzu tace  Alhmdlh yace  to Zan baki wani magani sau 1 zaki dinga  shan shi   Kuma inkika cire damuwar ranki zakiji sauki sosai tace insha Allah,

Doctor zan kiyaye yace yauwa zuwa gobe insha  Allah Zan sallameki,
Tunda naga jikin naki yayi sauki.

Yajuya yafita. Bayan fitarshi saiga  Meenat tashigo tace sister Safeeya tace Naam sister  kindawo  Meenat Eh Aidama ba nisa na dan mika kafana ne. Nan suka cigaba da firar su  har Umma tadawo  tayo ma Safeeya Abinchi ta daban na marar lafiya. Nan tadaure taci domin umma tace inbataciba  zata fada ma Abba,

 Washe gari


Da safe Doctor yashigo yaga jikin   Safeeya yaga  dasauki  yabata magani dasukayi Magana    yace taringa shan daya Arana Abba daban kan yatafi office  yabiyo   nan Doctor yake fadamasa yaga jikin  Alhmdlh zai bata sallama.

Abba yace babu damuwa.  Doctor yashiga ya rubutu takadar sallama  yabasu,

Abba yace suzo ya ajesu gida  sai yawuce office suka hada yan kayansu wadda sukazo dasu. Suka tafi

 Abba yanashiga gidan ko yana Ajesu yanufi office


Safeeya ko Suna shiga tazauna bisa kujera domin tace tagaji da kwanciya  bari ta dan zauna ta huta.  Basu jimawa da dawo wa ba,

Saiga Haidar yashigo  yayi sallama ya iske umma da Meenat saffeyya, saffeyya naji sallamar shi tayi saurin rintse idanuwanta Kamar me bacci.,

Umma tace haidar Kaine shigomana   ya durkusa cikin ladabi yace umma Ina kwana, tace lafiya lau, haidar, ya wurin mamyn taka dajikin yace  Alhmdlh Ankwace daurin yanzuma taka kafar Amma ba sosai ba umma tace Ai sai A hankali Allah yakaro sauki. Yace Ameen umma,

Haidar yace  yajikin safeeya ne naso zuwa wallahi umma   Aikin office ne yayi yawa  dayau zance Sai naga shigowarku Abba ya. Ajeku.
Umma tace babu komai Haidar,
Dasauki sosai tunda An sallamemu  taji sauki. Umma tawaiwayen inda saffeya take Safeeya!! Safeeya!!!!
Cikin Alamun Kamar tana bacci naam umma  tace Haidar ne yazo ganinki. Cikin daure  fuska tace Ina kwana yaya Haidar cikin Fara' a yace lafiya Lau saffeyya  yajikin tace Alhmdlh, daganan bata karacemasa komai  sai da Meenat yake fira jefi jefi har yamike yatafi,

Dama umma tashiga ciki tadan gyare gyare kwana biyu  baiga gyaraba.

Meenat tadawo kujerar da Safeeya take sister wai meyahadaki da yaya haidar baki sakar masa fuska   ne, saffeyya tace babu komai keh tajawo wata first




School


Dr Ahmed ne zaune bisa kujera yana hada wasu file  yaduba Agogon Hannusa yaga lokacin shiga lecture yayi, Kuma class dinsu Safeeya zaya,  yanashiga yagama Abinda yake, Amma da kalleshi kasan yanacikin damuwa ( Abinka da miskili)

Yanufi office yazauna yace meke damun wannan yarinyar yau kwana3  batazo school ba ko yar uwata banganiba    gashi yau Friday.

Gaskiya rannan Monday inbatazoba Zan tambaya wadda naga  Suna zama  tare naga ko lafiya duk wannnan Maganar yanayinta cikin zuciya


Domin yanzu so  safeeya kawai yaji yana shigan zuciyarsa ( Tofa su Dr Ahmed Anshigo wajen)

Domin ko ga basma baijin wannnan beyi hakaba


Muje zuwa dai😘😘😘😘




For comment

08164042255
[1/17, 1:24 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔
        Na

Hafsat (Hafsy baby)


15





Safeeya ce kwance bisa gado tana tunanin yadda zata fidda son Dr Ahmed cikin ranta,.

Amma  me datafara tuninshi zataji Kamar Anakaramata son shi naji take Kamar tajawo Ranar Monday.  Taje school don kawai taganshi, Amma tayi Mata kanta Alkwali zata ragema zuciyar ta tuninshin insha Allah,


Meenat tace shigo dakin datake sister  Kizo inji Umma ga girki can Angama, safeeya ta yatsina Fuska Kai sister Abinchin nan basai Anjima zanci ma Meenat tace A,a umma tace nataso ki har muntafi tare,


 Badon safeeya nason cin Abinchi ba ta  mike suka nufi Dinning,  tadan tsakura ta mike.

Bayan Abba yadawo  ne   baya shigowa sai yayi sallar ishai to inyashigo Bayakara fita sai kuma gobe. Inba wani Abu mai muhimmaci ba ne zai fiddashi.

Abba ya shigo yatambayi safeeya yajikin tace Alhmdlh Abba,    yace yauwa dafatan dai kinacin Abinchi sosai.

Meenat tayi karaf tace Abba bataci sosai dan kadan kadan takeci. Safeeya ta wurga Mata harara tace karya take Abba inachi sosai. Anya kuwa tace Allah kuwa. Yace inma yadda Meenat tafada ne kidaure kidinga ci kinji ko. Tace shikenan Abba,

Abba yajuyo wurin umma yace ke babu Abinda zakicene Umma yan biyu tace Babu Abinda zance ni.,   Nan dai sukayi firarsu Kamar kullum har lokacin  tashi yayi kowa yatashi yanufi makwancin sa. Asuba tagari.

Monday.

Monday babbba Rana ko nasara na tsoranki.,


Kamar yadda suka Saba sukatashi suka Kimtsa suka gama Abinda suke sukayi wanka. Amma jikin safeeya suku suku.  Kamar  marar laka jiki Har dai Meenat ta Lura da hakan
Tace sister yane naga kin koma wani kalan kina komai A hankali ne

Safeeya tace babu komai  Meenat tace Anya ko Safeeya tace Haba babu komai, Meenat taja bakinta tayi shiru,.

Safeeya kuma tunanin take yadda yau yazasu kare Dr Ahmed ne  yau kuma dame zai zo Mata ne
Shine jikinta duk yayi sanyi. Haka har Meenat tayi Mata Magana.


Sun shirya saffeya tayi shigar Atamfa  yellow And red tadora hijab yellow domin red din yafi yawa cikin Atamfar shine saita Dora yellow hijab,


Masha karkuso kuga yadda Safeeya tayi kyau gashi dama rashin lafiya datayi fuskar tayi fayau.
.


Ko Meenat sai datace   Masha Sister kinyi kyau Wallahi. Safeeya murmushi kawai tayi

Nan suka fito suka gaida umma da Abba sukayi Break fast,  sukayi masu Allah yakikaye  suka fito sukaja mota suka nufi school.

Daidai   su shigarsu school da  mota  shima Dr Ahmed ya shigo. Sukayi parking   suka fito  fitowar su  Idon Dr Ahmed yakai   Kansu  yakara waiga yaga itace dai ba idonsa ke masa gizo ba( su Dr Ahmed😀😀)



Yaga sun nufi class  wani dadi ya ziyartamasa zuciya kaganninta kawai dayayi .

Kagagere yake karfe 1: 30 pm

Domin sai sannan yake da Ajninsu. Don kawai yaganta .



Karfe 1: 30 student sunyi sallah sun dawo

Kamar jira yake kawai saigashi yashigo    cikin yanayi daya Saba shigowa ( miskili kafi mahaukaci)


Amma Abin kadan yawaiga wajen da Safeeya take  zaune can Dr Ahmed yagama Lesson. Yana tambaya kawai yatada Safeeya Gabanta yafadi ya jeho mata wani question,  Allah yaso ta iya wurin tabashi Amsa tiryan tiryan
Cikin Harshen turanchi,
Dr Ahmed yace what is your name?? Saffeyya my name is Safeeya  Suleiman, ok sit down class kowa ya mamakin tambayar  sunan Safeeya dayayi  Amma kowa dai yayi shiru.


Yana gamawa Abinda yake  yace Gobe zanyi test  yasa kafa kawai yafita.


Dr Ahmed daganan mota yaja yafita yanufi gida  yana shiga  ya iske  hajiyarsa bata falo dakinsa kawai yanufa yasakarma kanshi shower. Yafito  domin jin kanshi yake cikin nishadi.   Muryar Safeeya kawai dayaji.

Abangaren Safeeya kuma mamakin Dr Ahmed take yadda yayi Mata yau take . murna kawai take wannnan maganar dayayi Mata taji zazzzkar murysa.kowa ya fahimci tana cikin farin cikin



Washe gari.

Su Meenat sungama shiri kamar yadda suke  Amma sunata sauri domin Dr Ahmed First, Kuma test zai musu,Agurguje sukagama  komai suka nufi school Suna shiga  class ko minti biyar baayiba yashigo.

Kowa yasan dai test zaiyi dama yanashigowa yarubata test yace minti 20 yabada, minti 20 nacika kowa ya kammala. Domin question din masauki. Yayi

Yawaiga wajen saffeya yace  kitttaroman kikai man office. Baijira Amsataba yafita.. Gaban safeeya nafaduwa  ta tttara   ta nufin office din tana  tunanin kowani  wulakacin zai Mata






For comment


08164042255
[1/18, 4:08 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON  SO💔
         Na

Hafsat (Hafsy baby)

16

Nasaudakar da wannan page din gareki ( Mumcy husnah)
Allah yakara lafiya.




Safeeya Gabanta nafaduwa tanufi office din Dr Ahmed Tayi sallama yabata izinin shigowa jikinta nadar nadar.

Tace sir ga papers din  OK, yasa Hannu yakarba  Yacemata thank you,   tajuya. Tafita

Dr Ahmed yabita da kallo  Har tajuya tafita,

Muryata kawai dayaji yasa shi wani farin ciki. Da nishadi.

Safeeya nakomawa  Meenat tare ta sister wani wulankacin yayi miki ne. Safeeya tace girgirza Mata Kai tace A,a.

Lokacin tashinsu school yayi  sunnufo zasu dauki  Mota  suga Dr Ahmed tsaye wajen Motar shi yana latsa waya,  har suka shiga suka tafi.


Nan ko Ba latsa wayar yakeba kallon safeeya yake Afaikace.  Har sukaja motar suka tafi. Sannnan shima yashiga tashi.(Ciwon so fa yakama Dr Ahmed)

 Abangaren Safeeya Kuma har suka isa gida datuno  Kalmar thank you,



Da Dr Ahmed yafadamata sai taji kawai cikin Nishadi, Har wani murmushi farin ciki take.



Suna zaune  Suna cin Abinchi Meenat kecema Safeeya  gaskiya sister nayi mamakin Dr Ahmed,



Safeeya tace wurin me  kenan, tace yadda yacanzamiki mana,

Rannnan fa har tambayar sunanki yayi, yau kuma harda cewa ki tatttara papers kikaimashi,

Bakiji yadda class Ake surutun hakaba Wallahi,

Safeeya saidai tace uhum sukacigabada da cin Abinchi, Bayan sun idar ne  lokacin   sallar La' asar ne suka tashi sukayi.

Bayan sungama sukadawo Falo. Suna Kallon AREWA 24

Suna shirin Muna  Kwarya


Umma dabaman batanan tafita zuwa  Gaisuwa matar Abonki Abba tarasu hadarin mota,




Bangare Dr Ahmed kuwa yana shiga gida ya iske hajiyarsa tayi tagumi  Har yayi  sallama  batasan yashigo ba,


Saida yazauna  yataba Hannunta Sannan ta firgita Ahh Ahmed yaushe kadawo ne, yace nashigo  ita sallama  bakiji Ba,   ne meke damunki Hajiya sai kawai yaga Hawaye sunbiyomata mata, Ahmed yace meke damunki ne Hajiya  harda  Hawaye don Allah  kifadaman kowani laifi na Aikata gareki bansani Ba,

Hajiya saudat tace babu Abinda kayiman Ahmed  Ina tunanin yan uwana Yaya sule, da yaya mustapha,

Tunkafin A haifeka rabon danasu idanuwana Basan suna da raiba ko sun mutu,   nan tabashi Labarin sanadiyar Batansu, Dr Ahmed yaja Numfashi yace  ki kwantar da Hankalinki Hajiya   insha Allah  inda rabon zaku hadu  zaki gansu. Nan ya kwantar. Mata da Hankali,


Yatashi yashiga ciki  yawatsa ruwa yayi sallar la'asar yahau gado. Yakwanta,

Yajawo wayarsa yakira Amininsa wato Hafiz, suka sha firar su irinta Abokai.

Bayan sungama wayar Dr Ahmed  yaruntse idanuwansakawaiyaga  saffeyya nayi mashi Murmushi, Dr Ahmed yayi saurin bude idonshi   yatashi zaune yace Meke damuna Kar dai ciwon so yazautani  ita batasan inayiba ( haka dai kace)


 Amma tayaya Zan furtamata ne can kawai naga  yayi murmushi  nikaina Hafsat basan mumrmushi meye ba.

Amma mujezuwa



Saffeya da Meenat ce zaune   Safeeya  nayima Meenat calabar   umma Kuma tana zaune  suna fira jefi jefi  Saiga maigadi yashigo yayi sallama   ya agaidasu  yace  Hajiya wai Ana Neman Hajiya safeeya waje  wani mutum yace nakira  mashi ita, saffeya tace ni Akace kakira, yace Eh,

Safeeya tace jeka kace batanan, umma takatseta tace jeka    Audu gatanan, Safeeya tazumboro baki   umma tace tashi kije bakisan ko wayeba kikasan koda meyazo tunda  baa taba Aikowa kikasan komeya kawoshi,  tashi kije Kafin  Abba Ku yadawo kinji  Safeeya tashi ta zuri hijab tafita Meenat tanata tsokanarta  tacemata iyee su sister Anyi kasuwa. Safeeya kamar tayi Kuka  har didiren kafufuwa, umma kina jinta fa, saida umma ta tsawatar ma Meenat sannan ta kyaleta,


Saffeyya kuwa tana fitowa    tanufi wajen motar dataganni kuma mutumin ya juya baya   bata fuskarsaba   tayi sallama aka Amsa sai taji kamar tasan muryar Amma kawai tashare cikin ranta tace tunda nayi sallama   nafita hakkin kowaye  bazan Kara magana ba tafi minti biyar tanacewa wannan mutumin dan rainin wayo ne fa zsnshiga gida. Kawai taga Anjoyo fuska waza taganni...




Kubiyoni 😘😘😘😘😘






For   comment
     08164042255
[1/19, 10:42 AM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔
          Na

Hafsat ( Hafsy baby)

17


Wannna page din  nasaudakar dashi gareku bisa Kaunar book dinan dakuke

Jameela Abdullahi
Maman fadeela
Maman Khadeejat
Nan group din YAR GATA FANSCULB.
Ya Allah yabar Kauna😘😘






Joyowar fuskar da Zaayi watazagani Dr Ahmed Safeeya tayi mutuwar tsaye tarasa bakin bakin Magana. Can dai tayi ta maza.

Sir... Inayini yace lafiya lau safeeya Kina  lafiya tace masa lafiya lau. Safeeya tace yallabai meke faruwa. Yayi murmushin dake karamasa. Kyau  Safeeya tayi mamakin  murmushi sa domin tunda take bata ba ganin murmushin sa ba.

Dr Ahmed  yace zakiyi mamakin ganina Safeeya  Amma ba Abin mamaki bane.

Safeeya cikin ranta tace kuma meke tafe dashi ne  yama Akayi yasan gidanmu.



Yakatsemata tuninin datake yace safeeya,  tace  Naam sir, yace kidaina kirana da wannnan suna kirani da masoyinki,  mai fatan zama Uban yayanki insha Allah,



Safeeya tawani firgita  tayi kasake kawai kamar marar rai, Dr Ahmed yace zakiyi mamakin haka  daga gareni. Domin kinga tsanar danayi miki cikin school, 

Safeeya bawani Abu yajaman tsanar kowace mace ba Nan yabata labarin soyayar sa da   Basma da irin yaudarsa datayimasa.


Yace daganan naji natsani  soyaya Kuma bana ra' ayi kowace mace,nadauka duk Haka suke,




Amma  Farkon ganin dake naji komai na nema yacanza daga gareni shine nadukkan yimaki Abu natsana konaji  ba sonki,

Amma zuciyata ta Karyata haka  gani  da kokon barata gareki. Duk wannan bayanin dayake safeeya hawaye kawai


Tana girgiza Kai tana tafiyar baya baya hartashige gida da gudu. Tabar Dr Ahmed tsaye.


Tana shiga ta iske su umma basu falo  sun shiga ciki Domin lokacin sallar magariba yakusa. Tazauna Bisa kujerar Nan tafashe dawani kuka, tace cikin ranta Dr Ahmed yagano inasonsa shine Zan  biyo wata Hanyar salon wulakanta tani ko shine zai ce yanasona karya ne basona yakeba yaudararata zaiyayi ya wulakantani,  Nan takara fashewa da wani sabon Kuma,


Cantaga bafa ita kadaice kar umma ko Meenat tashigo ba kuma hujjar dazata bada,


Tatashi tagoge  Hawayen ta tashiga cikin Domin taji Anfara tada sallahr magariba,


Tanufi  Dakinsu taddata Har Meenat  tadata sallah itama toilet kawai  tashiga tadaurayo Alwalla,  tadata sallah,


Bayan sun idar da sallah ne, sunyi Addu' a sun mike ne, Meenat tana linke Carpet, din sallah, tace sister wai waye yazo nemanki, mai Neman Kuka Anjefeshi da kashin Awaki.


Kawai saffeyya tafashe da Kuka tace wai Dr Ahmed yazo nemana, wai sona yake sister  kawai yazo ne yaciman mutunchi ya wlakantani,


Meenat tayi murmushin kawai tace sister meye ba Allah ne yakarbi rokonkibane, ya mallaka miki Abinda kikeso,


Safeeya ta figirt tajoyo wajen Meenat, tana manata Kallon mamaki, Meenat tace karkiyi mamakin jin maganar danayi miki sister,   

Tun wani lokacin da dadddre Kina sallah  naji kina rokon Allah, Akan Haka, 


Nayi mamakin dabaki furta mankahava, nima saina kyaleki,





Saffeyya taja wani numfashi,


Meenat tace. Abinda zakiyi kawai kiba Allah zabi kawai.  Tashi muje falo. Suna fitowa suka iske umma zaune,


Suma suka zauna  Umma tace saffeyya wayene yazo wurin ki dazu ne,


Kunya tarufe saffeyya tarasa yadda  zata fadamata,


Umma tace takadara, to da kinata sunne sunne baki zuwa, Ashe kinsan kowaye,
Saffeyya tace Allah A,a


Umma tace Ummm


Nan sukacugabada firar Har lokacin  sallar ishai  yayi sukayi,




Abba yadawo sukaci Abinchi. Lokacin bacci yayi kowa yanufi makawancinsa.




Bangeren Dr Ahmed kuwa  saffeya nashigewa gida tana Kuka  yafi minti biyar tsaye sannan yaja mota yafita, yana tunanin to me take ma Kuka, hakan meyafaru,




For comment

08164042255
[1/19, 10:45 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔
         Na

Hafsat (Hafsy baby)

18





Washe gari

Meenat da safeeya sukayi shirin school suka fito.kamar yadda suka Saba suka gaida iyeyensu,

Sukaja mota suka. Nufi school,



Bayan sunfito daga lecture ne waje 12:00pm suna zaune suna  Hutawa itada Meenat

Saiga wata Budurwa tazo tana wani yamutsa fuska yar class din safeeya ce Amma basu magana da ita

Saboda tacika wani girman ita bawani kyau kirkiba,

Tazo tsaya kere kere tana hura Hanci, cikin Ku wace safeeya ma  safeeya tace gani lafiya dai,??

Tace Dr Ahmed ne kekiraninki, tawani juya tafi tana murguda kugu, saikace Andora Diyar roba Zane, 



Safeeya tace bazan jeba, Meenat takseta A,a sister kitashi kije don Allah keki fada fa babu kyau wulakanta mutum tashi,


Kije pls. Inan inajiranki.

Safeeya tatashi tagyra zaman mayafinta tanufi office Din Dr Ahmed tanashiga tayi sallama.



Tace sir gani, Dr Ahmed yadago ya kalleta da Dara Dara idonsa,


Yace safeeya!!   Safeeya saidata lumshe ido Domin ji tayi babu wadda ya iya Kiranta sunanta  Kamar Dr Ahmed,



Yace jiya nataka naje Har gidanku  da tayin soyaya Amma banji komai daga   bakinka safeeya kinshiga Gida kina Kuka,

Ban miki bane, inbamiki kifadaman, Amma kisani zuciyata takamu da matsanaciyar Kaunarki safeeya burina kizamo Mata Agareni, pls kitaimaka zuciya na ba tunyau takamu da sonkiba,


Safeeya cikin shashekara Kuka tace  Sir basona ka,

Katseni saiyanzu zaka furta Kalmar So gareni  bazan taba yarda da maganarka ba wallahi, tajuya tafita tagudu,

Domin Ciwon sonshi yataso Mata gaba daya,

Saidata tsaya tagoge Hawayenta sannan tanufi inda Meenat take,

Meenat bata tambayi saffeya komai yafaru domin lokacin shiga wata lecture yayi,



Bayan sunfito Antashi school, suka nufi wajen mota  suka iske Dr Ahmed jingene jikin tashi saffeyya tayi saurin shiga Meenat tashiga,
Sukaja suka nufi Gida,


Dr Ahmed Kuwa  kuwa kawai yabi motar da Kallo har tafita, yace  Allah ka Agazaman  son safeeya na Neman yayi Mani Illah, cikin zuciyata,



Safeeya suna shiga Gate man, yabude masu suka shiga, sukayi parking suka  fito suka shiga ciki gidan suka iske Umma zaune,


Tana Kallon Wa' azin  Dahiru Usman bauchi,.

Sukayi sallama suka shiga      Umma tace Yan biyu Andawo sukace  Umma  mundawo mungaji wallahi, tace. Sai hakuri duka bakingin shekara daya Idaba,

Ku huta, sai Aure Kuma, suka hadu baki Kai Kuma munanan dakai,


Tace A, a naga Aurenku har dauki jikokina,
   

Suktashi cikin kunya suka shiga cikin,



Bayan sun dan watsa  ruwa suka fito domin cin Abinchi( dama sunyi sallah  school)



2 weeks leter. 



Safeeya fa tasa Dr Ahmed cikin wani hali domin duk inda yaganninta  yanzu  kwata kwata yadaina Ganinta,  kuma tana shigowa  school,


Kuma kodayashigo class saitayi yadda taboye dokar yaganta,

Domin ko idan suke parkin yanzu kodai surigashi zuwa koyarigasu, kwata kwata sundaina haduwa,

Dr Ahmed yashiga hali daurewa kawai yake,


Yau bayan safeeya sunfito daga lecture take ma Meenat zata dangewaya nanbaya, Meenat tace ki iske waccan baradar tanumamata domin zanduba wani books, 

Safeeya tanufi cikin makaranta inda babu mutane tashiga can baya inda ke da yalwatar ciyawa,


Ashe kan idon Dr Ahmed kawai yabi bayanta, tacikin taba shuka tanaji dadi kawai saitaji Kamshin Tureren Dr Ahmed ita har tarike turenshi tayi saurin juyawa tabar wurin  kar ya isketa,

Kawai taga mutum gabanta,yace safeeya menai miki kike Gudana nane, kintsani ne bantaba zato masoyi na zama makiyiba nayi fadamaki Hujjata Amma kinji yarda  Kince, wulakantaki Zanyi, shikenan  safeeya Zan kylaeki bazan takuramakiba kisoni Amma kisani zuciyata takamu da kaunarki yadda  baki zato sai Anjima,


Yajuya  yatafi ,  saffeyya Kuma tafi Minti 10 tsaye. Kamar Ankafeta,nan dai  tadaidaita natsuwarta,

Tanufi wajen Da Meenat tace ta taddata, Amma tanashiga cikin ma karanta taga wani gungun  students,

Tadda meenat tsaye  tace meke faruwa ne naga  taron student Meenat tace Dr Ahmed yafadi yazo shiga.

Mota safeeya tace Dr Ahmed , kawai tajuya tanufi wurin mutane kafin ta isa har mota tadaukeshi domin zuwa  Asibiti, nan ta durkushe tana  Kuka,

   



Kubiyoni😘😘


For
Comment
08164042255
[1/20, 10:36 AM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔
        Na

Hafsat ( Hafsy baby)

19


Meenat ce tazo tatada. Safeeya dake Durkushe tace  sister tashi kinga har fara waigowa Ana kallonmu kitashi pls,

 Muje kawai dama lokacin tafiya yayi, safeeya tamike Amma bata daina zubda hawaye ba,


Safeeya tace laifi nane sister Ashe Son Dr Ahmed yakemaan dagaske Har zuciyarshi,.


Nan tafada duk yadda sukayi dashi,  Baya gewayarta bayan school,


Safeeya tace sister nafara  tun lokacin mai tsawo tunkafin yafurta Kalmar so gareni,

Meenat  tace nasani sister shareki nake naga Bakison nasani, shiyasa nima nakyaleki,

Ko ciwon dakika kwanta Asibiti nasan ta dalinlishi ne,  Amma don naji Doctor yace Ulcer ne shiyasa nayi shiru nima,

Saffeyya takara fashewa da Kuka  tunowa datayi  Dr Ahmed na Asibiti kowane hali yake,


Meenat taja Hannuta  tace  zomuje plz sister, kidaina Kukan Haka,

 Taja Hannuta suka nufi wajen motarsu, sukaja suka tafi,gida

Bayan Kwana biyu.


School


Shiru babu duriyar Dr Ahmed, saffeyya fa tarikece ma   meenat Abu kadan tasamta Kuka, itabatasan Halin da Dr Ahmed yake ciki ba,




Suna zaune kamar yadda suka Saba, saigawata yar class din wadda suke mutuchin da ita suna gaisawa sosai,

 Tazo wurinsu sunfara  Firar ne  tace wai kunje Gano Dr Ahmed ne,   Meenat Tace A,a  mezai kaimu Allah yabashi lafiya kawai,



Zeenat wadda suke zaune tace Ai Ance,


General Hospital Aka kwantar dashi, Amma Dakin sarakai,

Room 11, Nima naji Maryam nafadima  ikram, kinsa  Maryam son Dr Ahmed take Amma besan tanayi ba,


Nan wani Kishi yataso ma safeeya bata Bari  Amma tagane ba,



Nandai sukacigabada Fira Har lokacin shiga wata Lecture yayi suka shiga,

Basu fitoba sai 6pm


Suka dawo Gida Gajiye,

Sukaci Abinci Amma safeeya turashi kawai take,

Badon dadiba,  Hange wani Hali Dr Ahmed kawai take,




Dr Ahmed

Dr Ahmed Kuma bayan yafito Daga wajen safeeya ne,  yaji zuciyarshi nazafi daurewa kawai yake, yazo shiga mota ne,  kawai yaji wani Duhu ya gifatamasa Jiri yakwashe baikara Samun kansa ba sai A sibiti,

Hajiya saudat ce tashigo Firgice Ganin Halin Da Danta yake, cewa take Ahmed Kai kadai gareni meke damunka haka baka fadaman ba,
     


Saiga Doctor yashigo yaganta tsaye kan Dr Ahmed, yace kiyi Hakuri hajiya zai samu Lafiya insha Allah, Ciwon zuciyarshi ne, yatashi,


Hajiya saudat tace ciwon zuciya!!! Doctor dama Ahmed nada nada ciwon zuciya,bantaba sanniba,

Hafiz yayi sallama yashigo dama sunyi waya yau kwana biyu Da Dr Ahmed yace zaizo yakira wayanshi kashe saiya shiga school sai Akafadamasa yana Asibiti,


Shine yatafo, Hafiz yace Hajiya Ina yini, bata Amsaba, tace Hafiz dama Abonkika yanada ciwon zuciya Amma baa taba fadaman ba,


Hafiz yace kiyi Hakuri Hajiya don Allah,

Nan yafadamata,    silar  ciwonshi tun lokacin da Basma, ta yaudareshi,

Amma yanzu bansan silar ciwonshiba, Amma yafadaman yana cikin matsala sainaxo,



Hajiya ta girgiza Kai tace to Allah yasawkke tunda gaka kaxo, Bara naje Gida nadawo,


Bayan fitarta,   da Kamar ,
Minti 30 Dr Ahmed yafarka,

Yaga Hafiz zaune,  bisa Kujerar Kusadashi, yace Hafiz, Hafiz yace kafarka ne, yace nafarka, Hafiz yace wai meke damunka Haka,

Nan yafadamashi komai,
Hafiz yayi dariya  Ashe ciwon So yakwatar dakai,

Wane unguwa saffeyya takene nan yafashi mashi gidansu  Amma dalibarshi ce,

Hafiz yace dalibar kace Ashema,Dr Ahmed yace taki Amincewa dahkan,


One week later,


Yau Hafiz, yakeson zuwa gidan su safeeya domin Dr Ahmed  haryanxu yaki mikewa, Kuma yasan saffeya ce matsalar,


Yabin kwantacen da Dr Ahmed yayimashi yashiga har ciki,yayi ma maigadin. Maganaa don Allah yace Ana Kira saffeya,Maigadin yashiga, ya iske Meenat da safeeya zaune falo yayi sallama


Yace Hajiya saffeyya kizo waje Anakiranki bata jirataji kowayeba tace jeka ganinan,

 Ta mike tazuri Hijab,Meenat tana kallon iko Allah, Meenat tace baki sanar da Umma ne, tace yanzu zandawo Haba,  tafito cikin fa' ra a duk daukarta Dr Ahmed.




For comment

08164042255
[1/20, 3:56 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔
          Na

Hafsat ( Hafsy baby)

20




Safeeya tana fitowa cikin. Murmushi da niyyar. Itama zata furtama Dr Ahmed tana sonshi itama,

Kawai tayi turus sakamakon taga bashi bane,

Hafiz yace saffeyya ko,

Cikin ba yabo ba fallasa tace,

Tace Eh, Mallam lafiya dai KO,

Hafiz yace lafiya lau,
Saidai  Laifin ki daya.

Safeeya tace mekenan , yace Kinsan Abokina kwanciya Asibiti  Yau kwana Goma,

Saboda ciwon sonki,

Safeeya meyasa bakisan Abokina ne,


Ahmed bashi da niyyar cin Amanarki ko kadan,

Kuma ba wulakantaki, fatanshi kizamo, matarshi,

Ahmed baya wulantawa kowa shimai taimakawa ne,

Yanzu haka baisan nazo nan ba yanacan kwance Kuma sanadiyarki ne,
Kitaimaka kije kiganoshi don Allah kowayaji sauki koyayane pls safeeya,

Safeeya tajawani numfashi cin Halin da Dr Ahmed yake, 

Tace shikenan zantambayi Abbana inyabarni zanzo,

Hafiz yace yauwa safeeya nagode,
Yanzu kibani number ki,
Yadda  kukayi saiki sanar dani,

Tace OK, bb damuwa, nan takaratomashi Numberta, yakirata, shima tashi tashigo ciki tata,


Sukayi bakwana tashige cikin gida,

Tanashiga ta iske meenat, tasaka Album din Umar m shareef, tana sauaren domin Meenat tanason Yan shareef,

Saffeyya tazauna jagwab Meenat tarage. Volume din wakar, tace sister mutumin ne,
 A,a Abonkinshi ne

Nantafada yadda sukayi
Meenat tace yanzu yazaayi muntambayi Abba,

Safeeya tace yauwa ga shawara mezaihana mucemasa wata kawarmu yar class dinmu Akwantar daza muje ganota,


 Meenat tace yauwa   kin kawo shawara,  sis,

Suka tafa. Saiga umma tashigo,

Tace Kukuma shewar mikokeyine, kamar gidan biki, sukace Umma babu komai,

Wani Abu Aka nuno shine muke dariya,



Bayan  Abba yadawo sunci Abinci, sunyi sallah,

Suka dawo falo,
Suka durkusa har kasa,
Abba dama don Allah, Gobe zamuje ganin wata yar Ajinmu Ankwatar da ita,  Asibiti,

Abba yace Allah yakaimu  lafiya,



Sukatashi Ameen Ameen  Abba, Sukatashi suka nufi daki,

Safeeya tace Bari nakira zamuzo gobe,

Washe gari


Yau weekend bamu school

Su safeeya suna zaune
Har wajen karfe 4:00pm

Sukayi sallah la'asar nanfa Akashiga wanka,  Akfito, karkusokuga yadda saffeyya keshafa wnanna Agogawanan

Harsaida Meenat takai dayimata magana, sannan tamiki tajawo wata Arabian Gown, black kai Masha Allah saffeya tayi kyau sosai,

Sukafito, suka iske umma zaune falo, umma tace safeeya wanannan Make up dinta Kamar zaki party fa,

Kawai tayi murmushi tace umma sai mundawo tace Adawo lafiya kar Akai magariba, sukace insha Allah,

Sukafito sukajaa mota suka nufi General Hospital, Dakin sarakai,

Bayan sun isa ne, saffeya takiraHafiz  tace Gasunan, sun I so,
Abangaren Hafiz kuwa Gaban Dr Ahmed yayi, kawai Dr Ahmed yaga yamike yace inazaka, yacemasa inazuwa Minti 2, Hafiz yafito Harabar Asibiti, suka tafo tare da su  safeeya,

Toro kyaure daakyi ne yasa  Dr Ahmed yazabura....

Tofa KUBIYONI.

 ILOVE YOU ALL MASOYANA😘😘😘



For comment

08164042255
[1/20, 11:39 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔
        Na

Hafsat ( Hafsy Baby)

21





Toro kyaure Akayi Dr Ahmed kawai yawaigo yaga waye yana waigowa  Hafiz bayanshi,

Safeeya ce Dr Ahmed yatashi zaune, yamurza idonsa, Hafiz Ciwon so zai zautani kaga safeeya tafaraman Gizo,Idanuwa, KO

 Hafiz yace ba gizo takemaka itace dakanta,


Safeeya tarakube Kamar tanajin tsoron isa wajen shi, Hafeez yace safeeya ki matsa kiyimasa yajiki mana,

Saffeyya tamatsa jikin sanyi. Jiki,

Sir inayini, yakarfin jikin,

Yace naji karfin jiki tunda idanuwana sunganki, safeeya,

Meenat tatoro kofa tashigo,
Cikin sallama,   ta tsaya wajen domin ganin wata yar yar school dinsu Ankwatar da mamansu Asibiti,
Shine natshiga ganinta Kusada dakin Dr Ahmed,



 Meenat tamatso itama tayima Dr Ahmed yajiki.

Dr Ahmed babu Abinda yake ko sai Aikin kallon safeeya dayake,tadago idanuwanta saitaga sunhada ido,




 Hafeez yace safeeya tunda gaki kinzo kihadamasa ko tea ne yasha, Domin Hajiya fama take dashi yakinci komai,
Safeeya kawai saidai tayi murmushi,

Hafeez yace Meenat mudan basu wuri kila sunfi sakewa Ko



Meenat tayi dariya Aikuwa, suka fito,


Dr Ahmed yace safeeya kiyarda ba son yaudara nakemakiba,


Son tsakani da Allah nakemiki kidaure ki karbi soyayata, safeeya don Allah,



Safeeya ko sunne fuska kawai tayi bata bashi Amsa ba,

Yace safeeya baki Aminche bane, safeeya saidai ta sunno fuska tayi murmushi,

Domin cikin ranta wani dadi takeji Allah ya. Amshi  rokonta, Dr Ahmed nafurtamata Kalmar so vatare dayagane tana sonshiba,

Allah shine Abin godiya, tagodemashi,


Dayabata soyayar Dr Ahmed    Cikin sauki,

Saffeya tace sir Ance bakacin komai,Bari nahadamaka,   ko  Tea ne, Bata jira Amsar shiba tamike, tajawo plastic din ruwa zafi ta tsiyayi ruwa zafi dama Akwai Lipton, cikin gashi yaji kayan Kamshi sai tashi yake Bata sa madara ba kawai sugar tasa, tamika masa,


Sir gashinan kadaur kasha pls,

Dr Ahmed yakarba, yanasha yana kallon safeeya saidai kawai yaga Cup har yashanye,


Meenat ce tashigo tace  Sister muje KO, kinsan umma tace karmu Kai   magariba, Gashi takusa Kuma,


Safeeya tamike cikin sauri domin ita ganin Dr Ahmed ta manta komai,

Dr Ahmed ya maraice Fuska yanzunan tafiya zakiyi,

Safeeya cikin shagwba dabatasan tana da itaba sai yanzu,  tace kayi Hakuri umma tace karmu dade ne( Amma bata fadamasaba tace bawurinshi zasubo,

Yace Shikenan Cikin maraicewa ,


Tace sai Anjima Kakula da cin Abinchi pls,

Suka fito itada Meenat , Hafeez yayi musu rakiya har wajen mota, Sannan yadawo,

Dr Ahmed ya iske zaune yace yayi Hafeez yayi turus,

Yace   patient din dake kwance yana ni shi kadan kadan yau shine zaune,

Dr Ahmed yace Abokina, suka fadaman ya akayi naga safeeya taxo ganina,

Hafeez yace naga itace maganin ne, shiyasa nabi Address din dakabani har gidan su,nan yafadamashi yadda sukayi,

Har musaya number dasukayi,




Safeeya kuma su isa gida Anfara kiraye kiraye, sukayi parking suka fito, suka shiga cikin basu tadda umma falo sun tashiga Sallah,   suma daki kawai suka nufa subada tasu.




ILUV YOU ALL MASOYANA

INASONKU FIYEDA YADDA KUKESONA DOMIN DABAZAR KU NAKE TAKA RAWA, LOVE YOU ALL😘😘
 


For comment

08164042255
[1/21, 10:14 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔.
          *Na*
     *Hafsat*(Hafsy baby)

22





Bayan su Meenat sungama sallah, ne suka zauna suna fira  can wayar saffeyya tayi Kara  dubuwa tayi taga  Haffez ne yake kiranta  tadaga tayi Sallama tace,

*Assalamu,Alaikum* *Haffez* *yace* *Ameen* *Walaika,Salam* *Saffeyya* *Kun* *Isa* *Lafiya*

 Safeeya tace lafiya lau, wallahi muka isa,  Hafeez yace Alhmdlh Ahmed dama ya ishini  dama sai nakiraki  yaji kun isa lafiya, saffeyya umm kawai tace yacega Ahmed din.


Dr Ahmed yakarbi wayan hello safeeya, safeeya  ta lumshe ido Domin jindadin kiran sunanta dayayi.

Sir, yarkafin jikin bazan Amsaba  banace kidaina Kira da sir ba  safeeya tace  *sorry* zandaina  yajikine,

Dr Ahmed yace Alhmdlh tunda naganki naji sauki  safeeya kisani  inasonki, Ina Kaunarki,  Kifurtaman Nima  konaji sanyi  pls My dear, safeeya tayi shiru, can Kamar minti 2 Dr yaji shiru, yace Hello safeeya bakijina safeeya tace  inajinka  yace pls Kifadaman safeeya tace  Inasonka!!! Dr Ahmed  tayi saurin katse wayar, 




Abangaren Dr Ahmed Kuwa yanajin  wanannn Kalmar  Daga bakin safeeya ta Aminche  tana  sonsa ya wani rungume  Hafeez  Dama yana kusa dashi


Yace Hafeez safeeya ta Aminche tana sonsa  yasaki  Hafeez, yadaga  Hannu Sama, Allah nagodemaka  Allah  Abin Godiya,

Toro kyaure  Akayi  Doctor yashigo zaiduba  jikin Dr Ahmed  Amma sai yayi turus  Ganin Dr Ahmed zaune  Bisa Gado  yana murna  Hafeez yace Doctor muhsin  yakayi  tsaye  kakaraso mana,  Doctor muhsin  yace mamaki   nake  patient din dake kwance   Numfashi Sama sama yaushi  ne zaune  Bisa gado yana murna,

Hafeez yace dama *CIWON* *SO* ya kwantar   dashi yan ya mike  Kagako ciwon ya kwantarshi,

 Yanzu An Aminche Anayi dashi shine ya mike, kagago  Ciwo ya warke  Sai Abamu  sallama ko Doctor muhsin  yace  nayarda Babu Abinda  so basawa.

Nan yakara dubashi   Yaga komai Normal
Yace to komai yayi sauki  Dan love, Gobe Insha zanbaka sallama,  sai Aje Acigabada da love


Dr Ahmed yayi dariya kawai


 Saffeyya kuma tana katse wayar  tafada Bisa gado  sai murna  Yau Allah  yacikamata Burinta  Yau gata wai soyaya da  Dr Ahmed ( Abin Allah kuma)


Meenat tadamata duka  to Juliet,  tashi muje  falo ko Umma taga mundawo  ko

Nan saffeyya ta mike suka nufi Falo suka iske umma zaune sukace Umma mundawo  lokacin kinshiga sallah,


Umma tace naji shigowar ku, kunganota yajikin Nata sukace Alhmdlh taji sauki sosai umma tace to Allah yakara sauki  Ameen. Ameen Umma,





Bayan Abba yadawo ne Akaci Abinchi Akazauna Falo Har lokacin tashi yayi  kowa yanufi makwancin sa,
Saffeyya tanashiga  tanufi wayanta datasa chaji  tasan tacika  tana latsawa taga 5 Miss call, da wata new number  kawai tashare tazare wayan tanufi bisa Gado,tana zama kamar jira Ake Saiga wani kiran yashigo  dawannan new number kamar bazata daukaba kawai tadauka,

 Tayi shiru , hello safeeya   tamike Daga kishidar dayayi jin muryar Dr Ahmed yace inakikashiga  inatakiranki
Tace Ina falo yanzu  nashigo naga kiran  Ganin new number shiyasa bankiraba

Dr Ahmed yace number tace   yanzu na Amshi taki wajen Hafeez

Nanfa  suka Fara fira tun saffeyya tanajin kunya Kalma da Dr Ahmed kefadamata  na soyaya  hardai taware( dama me Neman kuma)



Bayan sungama badan yasoba yayi Mata magana  domin chajin shi yakare,

Saffeyya ta waiwaya wajen Meenat taga Har tayi bacci Nan itama tajawo bargo   tayi Addu' a ta lumshe ido cike da farin ciki da Annushuwa.




*Kutayani* Addu' a *yau* *bana* *lafiya* *Wallahi*


*I love* *you* *All* *masoyana* 😘😘😘
[1/22, 9:12 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔```CIWON``` SO💔
         Na
 Hafsat ( Hapsy baby)

23




*Bayan* *sati*  *biyu*



Soyaya tayi nisa tsakanin Dr Ahmed safeeya kowa nuna kowa so yake tsakninsu,

  Ko cikin class inda yadinga kallonta har sai ta kauda fuska,

Har ya class basu  fahimci komai ba har  suka fahimta,

Kowayasan soyaya suke da Dr Ahmed nan fa Akafara magana Dr Ahmed yana soyayya da safeeya,

Kusan students wata Rana ma suna zaune  saidai azo Ace kunga yarinyar Dr Ahmed wadda suke sonshi Amma basu gabanshi,




Dr Ahmed zaune cikin Gidan su safeeya suna   fira  suna cikin Farin ciki da Annushuwa,


Irinta masoya wadda kamar sun shekara din,nan tare,



   Kawai Saiga Haidar yashigo yace safeeya saboda wannnan dama kike wulakantani baki saurerena,
 

Kiki dan uwanki  saboda bare ko, yayi kwafa, kawai yawuce,

Dr Ahmed yajiyo wajen saffeyya yace waye wannan, tace, yayana ne dan kanen Baba ne, yace kinaga babu matsala kuma tace babu, komai nan suka cigabada da firarsu ta masoya,


Har lokacin tafiyarshi yayi yatafi



Soyaya fa tamika tsakaninn Dr  Ahmed  Da safeeya babu Kama Hannun yaro,

Haryana fadamaata sai Aiko Gidansu domin Ayi maganar manya,



Safeeya ce zaune falo tana kallo  Meenat tashiga dakin domin yi sallah, itakuma saffeya tana fashin sallah,


Kawai sai haidar yashigo yayi sallama  safeeya kawai tana Amsawa taga shine, kawai  takauda fuska tacigabada Kallo,


Haidar yazauna yace safeeya wai menayimiki ne tunranar Dana  furta Kalmar so gareki,  kika canzaman pls, kifadaman.


In Akwai Abinda nayi miki kifadaman  sainacanza inasonki, safeeya nifa dan uwankine,

Safeeya tace yaya Haidar babu Abinda kayi man zuciyata  tana tare Dr Ahmed  kayi Hakuri Kanemi wata



 Akwai Mata cike dagari  kalaa Kalaa masu kyau wadda suka fini komai  kaje  kanemana,


 Tanaciki wannan maganar wayanta yayi Kara tana dubawa taga Heart beat,

Murmushi kawai tayi tadaga wayan,



Hello sweet heart,  tajuya tashige daki  tabar Haidar zaune,




********************************************************



Safeeya ce tsaye Gindi mirror tana shafe shafe domin Dr Ahmed yacemata yanan tafe Yanzu,

Meenat tacema safeeya Kina ganin haka zaiyuyu Abba besai Dr Ahmed yana xuwa wajenkiba haryanxu ba

Baki gudun wata Rana ya iskeshi ne,

Safeeya tanashafa janbaki Abankita,

Nida Dr Ahmed mun yanke shawara lokacin dazanfara Exam zai Aiko iyeyensa,

Lokacin dazan gama bautar kasa, saikawai Adaura mana,

Aure ko, Meenat ta girgiza Kanta tunda kinga haka yayi shikenan,

Wayar safeeya tayi Kara tana dubawa taga Dr Ahmed dauka tayi tace ganinan my dear,
Takatse wayanan, tadauki Hijab dinta tazura ta nufi Hanyar waje wurin sahibita Dr Ahmed,


Sun Fara fira irinta masoya

Kawai safeeya taga Anwangale Get motar wazatagani motar Abba kawai tagani

Gabanta yayi mummmuanar faduwa,


*KUBIYONI*😘😘
[1/22, 9:54 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔```CIWON``` SO💔
      Na.

 Hafsat (Hapsy baby)

24








Motar Abba tasanyo kai tashigo tayi parking,

Safeeya gabanta yanata faduwa domin tayi mamakin dawowar Abba yanzu, baci bayanzu yake dawowaba,



Abba yawuto zaishiga ciki Kallon saffeya kawai yayi yashige ciki, Dr Ahmed nagaidashi Amma bai   tsaya saurenrenshiba


Yashige ciki  Dr Ahmed yace saffeya inagaida Abba Amma be Amsaba fa,

Saffeya takakaro murmushin dole, domin Gabanta keta faduwa,

Tace baijiba ba,  Dr Ahmed  yace Kila yaduba Agogo yace zanje,


Domin nafadamiki Akwai inda nikeso son zuwa, sai munyi waya, KO,

Safeeya taceshikenan sai munyi waya nan sukayi bankwana tashiga ciki,




Abba Kuma yanashiga falo ya iske Umma zaune, tana Kallo,

Saudat waye saffeya ketsaya dashi batare dasaniba, An rairnani kenan,

Umma tace safeeya domin Umma ita har Ga Allah batasaniba    domin duk lokacin da saffeya kefita batasani tun lokacin

Datacemata tafita taga waye kenemanta,

Tunlokacin tadauka maganar ta wuce

Yace Eh yanzu naganta dawani tsaye  mana,



Waje suna fira,

Safeeya ce tayi sallama tashigo,

Abba yacemata safeeya waye kikaba umurni yazo wajenki batare dasaniba,

Korainani kikayine??

Safeeya tadurkusa har kasa A,a Abba bahakabane wallahi, dama   Bari nayi  mufara Exam  zanyi maka magana


Kayi Hakuri don Allah  Abba


Abba yadakatar  da ita da Hannu yiman shiru   mutuniyar banza,



Tokisani Kinada miji jira nake kigama exam  asa Rana,

Dakin dawo Bautar  kasa sai biki.

Banyi niyyar fadamiki yanzuba  Amma zanfadamiki tunda naga wani na niyyar shiga rayuwarji,


Vawani bane face Haidar,

Domin munyi niyyar Hadaku Aure nida mustapha,

Saffeya tazaro ido Abba haidar,

Yace Eh,

Tashi kibani wuri.

Tofa😳😳😳


*AMMA* *MUJE* *ZUWA*

*Luv* *you* *masoyana*😘😘
[1/23, 1:12 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔```CIWON``` SO💔
           Na

Hafsat ( Hapsy baby)

25


® *P*. *W*. *F*.


Safeeya tana mikewa daki tanufa tagudu  tashige meenat tana chart da friend dinta awaya taji shigowar  safeeya tana Kuka,
Aje wayarta tayi Arazane tace meyafaru sister me akayi kinfita lafiya kindawo kina Kuka meyafaru,
Safeeya tanafada jikin Meenat tace Abba. Zai hadani Aure  da Haidar zai rabani Dr Ahmed wayyo sister sai  kuka😭😭 kamar Anbude famfo.

Meenat tahau rarrrshin safeeya,kiyi hakuri sister  don Allah kiba Allah zabi kiyi hakuri don Allah,

Meenat tanacikin ta rarrshinta saiga umma tashigo itama ranta bace yace  kukan me zakiyi komai yafaru kikajamakakanki,
Wai Ashe har fita kike badasaniba, kifita wajen saurayi ke kuma Amina kona kallon kinsan Abbanku bayayarda Amma kika kyaleta koki fadaman ko,  Meenat ta sadda tadakai, umma tagama, fadanta,  tafita, safeeya takara  fashewa dakuka kamar me Meenat tararrashin Amma takiji, kawai  itama  kawai saita fashe da kuka.
Can sunacikin kuka wayar saffeya tana Kara tana dubuwa taga  Dr Ahmed ta aje to mezatacemasa,  tana dubawa taga 5 miss call  tashare hawaye tadauka  tana dauka yace saffeya meke faruwa, kawai  kuka yazomata kashe wayar tayi bakidaya  ta cillar da itah,

Abangaren Dr Ahmed kuma safeeya kuma yana tana kashe wayar yanakara Kira yaji switch off,
Yamike yafara Kamar wadda Aka yace tomeke faruwa ne haka yana ta try, har yagaji,
Yakoma yazauna sai gumi, yake kamar wadda yahadiyi kunama,

Saffeya kuma dare yayi umma tazo kiransu ta iske Meenat tana sallah saffeya kuma tashiga toilet, har tajuya, zata fita saffeyya tafito, umma tace inkugama kuzo ga Abinchi, yana dinning, saffeya tace nina koshi, Umma tace dama kinsaki ranki, wallahi domin kinsan hali Abbanku da kafiya tajuya tafita,

Bayan meenat tagama sallah tajoyo wajen da saffeya  take   tayi tayi tagumi,  tataso taddata tace sister don Allah kiyi hakuri kidaina sa zuciyarki pls,

Tasomuje falo nan tataararasheta suka  nufi,
Saffeya yayagar Abinchi kawai tayi ta mike zata tafi.
Abba yace ke dawo inada Magana dake safeeya tadawo Abba yace Haidar zaifara zuwa wajenki don Ku fahimci, Juna, kafin Aurenku, shima inmukahadu office Gobe zanmishi magana jeki,
 Safeeya taruga da gudu daki domin wani kuka yazomata, tanazuwa tafada Bisa gado sai kuka, Daren da bacci yana 💔```CIWON``` SO💔
           Na

Hafsat ( Hapsy baby)

25


® *P*. *W*. *F*.


Safeeya tana mikewa daki tanufa tagudu  tashige meenat tana chart da friend dinta awaya taji shigowar  safeeya tana Kuka,
Aje wayarta tayi Arazane tace meyafaru sister me akayi kinfita lafiya kindawo kina Kuka meyafaru,
Safeeya tanafada jikin Meenat tace Abba. Zai hadani Aure  da Haidar zai rabani Dr Ahmed wayyo sister sai  kuka😭😭 kamar Anbude famfo.

Meenat tahau rarrrshin safeeya,kiyi hakuri sister  don Allah kiba Allah zabi kiyi hakuri don Allah,

Meenat tanacikin ta rarrshinta saiga umma tashigo itama ranta bace yace  kukan me zakiyi komai yafaru kikajamakakanki,
Wai Ashe har fita kike badasaniba, kifita wajen saurayi ke kuma Amina kona kallon kinsan Abbanku bayayarda Amma kika kyaleta koki fadaman ko,  Meenat ta sadda tadakai, umma tagama, fadanta,  tafita, safeeya takara  fashewa dakuka kamar me Meenat tararrashin Amma takiji, kawai  itama  kawai saita fashe da kuka.
Can sunacikin kuka wayar saffeya tana Kara tana dubuwa taga  Dr Ahmed ta aje to mezatacemasa,  tana dubawa taga 5 miss call  tashare hawaye tadauka  tana dauka yace saffeya meke faruwa, kawai  kuka yazomata kashe wayar tayi bakidaya  ta cillar da itah,

Abangaren Dr Ahmed kuma safeeya kuma yana tana kashe wayar yanakara Kira yaji switch off,
Yamike yafara Kamar wadda Aka yace tomeke faruwa ne haka yana ta try, har yagaji,
Yakoma yazauna sai gumi, yake kamar wadda yahadiyi kunama,

Saffeya kuma dare yayi umma tazo kiransu ta iske Meenat tana sallah saffeya kuma tashiga toilet, har tajuya, zata fita saffeyya tafito, umma tace inkugama kuzo ga Abinchi, yana dinning, saffeya tace nina koshi, Umma tace dama kinsaki ranki, wallahi domin kinsan hali Abbanku da kafiya tajuya tafita,

Bayan meenat tagama sallah tajoyo wajen da saffeya  take   tayi tayi tagumi,  tataso taddata tace sister don Allah kiyi hakuri kidaina sa zuciyarki pls,

Tasomuje falo nan tataararasheta suka  nufi,
Saffeya yayagar Abinchi kawai tayi ta mike zata tafi.
Abba yace ke dawo inada Magana dake safeeya tadawo Abba yace Haidar zaifara zuwa wajenki don Ku fahimci, Juna, kafin Aurenku, shima inmukahadu office Gobe zanmishi magana jeki,
 Safeeya taruga da gudu daki domin wani kuka yazomata, tanazuwa tafada Bisa gado sai kuka, Daren da bacci yana barawo yasace safeeya , yasace safeeya kawai,






                       26




Washe Gari


Sun shirya Kamar yadda suka Saba Amma daka Idanuwan safeeya sun kumbura domim Kuka datasha jiya. Saffeya tadan sha ruwa tea kawai suka nufi school

Suna parking Dr Ahmed Yanacikin mota yaga safeeya bata cikin faraa kuma idanuwanta sunyi, ja,

Bayan su saffeyya sun fito Daga lecture farko tana zaune itada Meenat Amma saffeya tayi tagumi    tana cikin tunani kawai wayarta tayi Kara taduba taga Dr Ahmed  dauka kawai tayi bejira tace komai yace kiddaatani office, yaktse wayar,saffeya kawai tamike tacema Meenat inazuwa,

Tanufi office din Dr Ahmed.
[1/23, 5:04 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON. SO 💔
         Na

Hafsat ( Hapsy baby)
P*. *W* . *F*

27





Saffeya tana shiga office din tayi sallama yace shigo,  saffeya tashigo cikin sanyi jiki Dr Ahmed yanunamata Kujera tazauna yace   zauna safeeya meke faruwa nake kiranki baki dauka ne  tunjiya karkiso kinga  Halin danashiga pls meke faruwa don Allah safeeya tadago idonta wadda yafara hawaye,

Yace safeeya meke faruwa don Allah kinga hankalina yatashi daganin hawayenki,

Safeeya kawai kamar A kunnamata inji kawai takara fashewa, dakuka saidatayi me isarta, sannan tagoge fuskarta sannan tadago fuskarta tace Abba zai  Hadani Aure da  Haidar

Dr Ahmed yamike tsaye  cikin figita yace what!!!!!!

Waye  Haidar tace wadda rannnan muna tsaye yazo.
Dr Ahmed yaja wani numfashi idonsa yayi Kala yayi jajir Almun tashin Hankali.



Abba kuma bayan ya isa office kawai kiran Haidar yayi yace bayanzu  nayi niyyar fadaamka wata Magana Amma naga inbanyima tokar hanci ba.

Abaya munyi magana da mustapha zamu hada ka Aure da saffeya   tunda naga tun kiruciya jinin Ku yahadu .

Tonaga tafara tsaya dawani yaro bama danasani naba,

Yanzu xaka Fara zuwa wajenta don Ku   fahimci juna kafin ta dawo Daga bautar kasa sai Anfara shirye shirye,

Haidar dadi kamar me cikin  zuciyar  sa  jin zai mallaki safeeya cikin Ranshi.

Tashi kaje  Haidar yatashi yana sosa Kai yafita yana fa' a






28



Abuyayi yayi. Tsanani saffeya duk tarame bata cin Abinchi, sai yawan Kuka Amma Abba yace  komai zayayi baya canza mganarsa inma tana fidda ma kanta damuwa tafidda Aurenta  da Haidar sai Anyi.


Yauma kamar kullum tana zaune falo itada Meenat suna Kallo Amma safeeya hankalinta baya wurin kallo  tashiga tunani kawai, Haidar yashigo, Meenat kawai ta Amshi sallama ma saffeya   ma batasan yana iyiba, Meenat mikewa kawai tayi tashiga ciki.

Haidar yace safeeya   Amma batajiba  yabuga hannu kujera yace  safeeya!!!

Tafirgita tadawo Daga tuninin data tafi  taganin Haidar ne tabuga tsoki,
Tajuya baya.

  Haidar yace safeeya wai sai yaushe zamu samu fahimtar juna tsakanina  dakai kinaji dai Abba  sunriga sunyi Magana da daddy tsakanina dake sai maganar  aure   inkidawo dga bautar kasa    yakàmata   kisaranki don Allah

Kullum nazo wajenki baki tsaya ki kulani  Haba saffeya mikewa safeeya kawai tayi rike kugu kaga malam kadameni

Wai Ana soyaya dole nace banasonka Akwai wadda zuciyata keso don Allah ka kyaleni,

Tabuga tsoki tashiga
Cikin.

Haidar kuma binta yayi da ido hartashige murmushi kawai yayi yamike yafita.
[1/23, 8:09 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔
        Na

Hafsat ( Hapsy baby)

  29




Dr Ahmed yashigo cikin Gida ya iske  hajiya zaune tana lazimi  yayi sallama yashigo  yagaidata zai wuce, hajiya saudat tace yaka Ahmed.

Dr Ahmed  yadawo yadurkusa hajiya  yace gani hajiya, hajiya Saudat tajuramasa ido  tacemasa Ahmed kanada wadda tafini Aduniya  Dr ya girgiza Kai yace A,a hajiya,


Tace tomeyasa kake boyeman damuwarka Ahmed??

Cikin kwananan Ina ganinka cikin damuwa  sukukufa  vaka fa'raa  daka dawo saidai kashige daki.


Ahmed Kai kadai gareni  Aruyuwata  Amma kanasan kasanka cikin damuwa

Ahmed  kwanciyar ka  Asibiti Anfadaman ciwon zuciyane  gareka Amma  bantaba  nunamaka ba hafeez yafadaman komai.



Kuma yanzu meke damunka Ahmed, yadago  fuskar  yace  Hajiya safeeya  yarinyar  dazuciyata ta Aminta da kaunarta  ita zaayima Aure,

Abbanta zaihadata   Aure da dan kanenshi, hajiya inason safeeya ,

Hajiya taja  numfashi tace Ahmed hakuri zakayi  Ahmed kabarma Allah komai, shikeda iko Akan komai, kaji ko tashi Allah yayi maka Albarka,  Dr Ahmed yamike yace Ameen yashiga daki yana zuwa yafada

Bisa gado rakwacab, yaduba wayansa ya Kira safeeya kowayaj sanyi.

              30


Lokacin kuma safeeya tana falo  Abba yakirata yanacewa Anrago bikin domin Haidar yafadamashi, wulakacin dataakemasa,

Dasun gama Exam da sati ukku zaayi bikin dakinta tayi bautar kasa, tofa😣😣😣
Muje zuwa




Lokaci yana tafiya kwanaki sunaja saffeya yau kingi 1 week sufara exam Abu yahadema safeeya biyu.
Kowa ya ga safeeya sai yatausayamata tarame sosai sai fari kawai,

Shima Dr Ahmed kowayaganshi baya tare da walwalla tare dashi Abinka dama da miskili sai yakara kurma karfi dayaji.

********************************************************

Komai yayi farko zaiyi karshe yauga su safeeya  sungama Exam yau lafiya sunata pic din bakwana da yan makarantasu.


Domin wani saikadade bakaganshi ba wani ma har karshe rayuwa bazaka sake ganinshinba.


Amma kowa yaga safeeya bata cikin walwala Meenat ketajawo kota Saki jikinta Amma murmushin karfin hali kawai take,

Wayarta tayi Kara tana dubuwa taga Dr Ahmed kekiranta  tafita Daga cikin hayaniya domin tadaga  tace, hello, yace kisameni  nan bayan wajen office din Dr mukhtar,

Tace OK, ganinan takatse wayan bata koma wajen su Meenat ba kawai  inda yace tanufa, tanufi bayan tana zuwa
Ta iskeshi tsaye  yaharde hannuwa.


                  31



Tanazuwa Dr Ahmed yabita da kallo itama kuramasa Kallo tayi,

Sunfi minti 15 suna kallon junansu babu kyaftwa,

Dr Ahmed ya kauda idonsa yaja Numfashi mai karfi yace safeeya yanzu rabamu zaayi ko ki Auri wani bani ba,


Safeeya  Ina Kaunarki   sondaban tava iyima watashiba,  aryuwata,


Idan narasaki  Bansan Halin dazan shigaba  Aruyuwata,

Safeeya  wallahi idan narasaki  bazan taba  aure Arayuwataba  zanta rayuwata haka  har lokacin  mutuwa ta yayi.




Saiga Dr Ahmed yana hawaye Tofa ciwon so  Maisaa kuka  Dr Ahmed yamike.

Yace safeeya zantafi  sai wata Rana, saffeya tamike tace sai wata Rana????


Yace Eh, sai wata Rana  domin rabuwa dake yazama dole  safeeya saboda  maihaifinki, yazabamiki  miji



Safeeya tazo gabansa ta tsaya kokasan zuciyata bakuwar zuciya ce dakai tasoma soyaya,

Yazakazoma jaririyar zuciya dabatu irin wannan,

KO kasan  zuciyata kamar kwalba ne sonka Kamar  ruwane dayasshiga ya daskare inda zaa cire saidai Afasa kwalbar,

 Dr Ahmed yajuyo wajen safeeya ya muka iya
 Safeeya  muyi hakuri  da juna,

Safeeya nabarki lafiya  inayimiki fatan Alkairi


Yajuya yatafi  saffeya tabi bayanshi  tana kiranshi  Amma inah  bai juyowaba,

Domin hawaye ke tsiyaya  yake safeeya tazauna  kasa rarashe rashe  tana rufzar kuka .

Allah sarki so

Allah karabamu da ciwon so.



*Ina* *godiya* *masoyana*
*masu* *kirana* *DA* *masu* *iyiman* *text*

*nagode* Allah bar kauna😘😘😘
[1/24, 6:49 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔
         Na

Hafsat ( Hapsy baby)



32




Meenat ce keta joyo Joye inda zata ga  hango saffeya Amma bata gantaba Meenat tace to inatashiga ne.

 Nan tafito Daga cikin taron mutane tana dubuwa cantahango safeeya tana goge fuska da gyaletnta
Dasauri Meenat  ta isa wajenta,

Safeeya tana hango Meenat  ta isa wajenta dagudu  tafada jikin  sai wani sabon kuka yazomata,

Tace sister Dr Ahmed yabarni wayyo Allah na  yanayiman fatan Alkairi,

 Inayimasa magana betsaya saurerenaba,

Sister inason Dr Ahmed  Abba zai hadani da yaya Haidar.

Banason yaya Haidar  Meenat tace  don Allah kiyi shiru sister kibarma Allah komai,
 Shikeda iko Akan komai,

Nanta rarrrsheta tayi shiru suka dawo cikin mutane  har akagama  komai da komai. Kowa yawatse.





Shikam Dr Ahmed yana barin wajen safeeya  mota kawai yaja  yafita  Daga school,
 Allah kadai  yakaishi gida domin  Gudu kawai  yake,

Yanazuwa  kodaidata parking beyiba  yafito dakinsa kawai  fadawa yayi Bisa gado ko talkama be cireba,

Wasu hawaye masu zafi suka zubomasa  yace narasa  safeeya Arayuwata .


Basai lokacin daya dauka yana tunane tunane,


Wayarsa tayi Kara yanadubawa  yaga my best Friend,


Yadauka  yace Hafeez  dagacan bangaren  yace Abokina,

Yanaji  muryarka wani kalah,
Dr Ahmed yace  babu komai bacci ne nafara,


Hafeez yace dama zanfadamaka  nanda 2weeks zanshigo katsina   daddy zaifara ginin company. Nan sukayi magana ya datse wayar.



              33



Safeeya ce kwance daki ta rame sosai saikace ba saffeyya kukan yau daban na gobe dabam

Batacin Abinchi  tarame  sai kuka  hartakai data kuka zuci

Umma  tunbata  shiga  Al' amarinta  hartakai  data  bata tausayi,


Tana rarrrshinta  Abba yace  komai zatayi baza fasa Aurenta  da haidar ba.



Yanzuma kwance take tunanin wai yanxunan vazata Auri Dr Ahmed masoyintaba,

Meenat, ce tatoro  kofar daki tashigo  tazauna  wajen da safeeya take tazauna,


Tace sister  don Allah  kirage damuwarnan,
Kibarma Allah, kamar ba musulmaba,

Kidauki kaddara, mai kyau, ko marar kyau,

Jiyadda kika koma  kinrame  yanzu tashi muje falo  domin  idan tafadamata Haidar ke kiranta bazata jeba,


 Saffeya ta tashi  suka nufi falo. Suna shiga kawai taga Haidar zaune falo  kawai buge hannuta tayi Daga hannun Meenat ta buga tsoki  tashige ciki,




Meenat  tawaiwaya wajen  Haidar, tace kayi hakuri yaya Haidar,
Yace babu komai  Meenat  kyaleta,

Dama nazo naji  shirye shiryen Ku, Meenat tace  insun shirya zasuyimasa magana,

Yace babu damuwa, yatashi yatafi,

Meenat tashiga cikin dakin  cikin Fushi  tace sister  wai yakike haka ne  don Allah meyasa  bazaki hakura, da Dr Ahmed kisa  yaya Haidar,

Saffeya tawurgo ma Meenat harara kinga malama ya isheki  tsoki taja kawai tabar dakin ,

Tanufi waje tana try, din number Dr Ahmed  domin tuneanar dasuka rabu  school, haryanxu batasake samunshiba,
Harda hakan yakarasata damuwa,
Shikam Dr Ahmed  yacire Sim din dasuke waya da saffeya  kowa yaji saukin  wani Abu, domin. Inyanajin muryarta  zai shiga matsala, babba,

               34



Lokaci yana tafiya kwanaki suna Kara yawa, yau bikin  saffeya da Haidar kingi kwana goma,  Amma babu ruwanta  dawani hidima  biki  Meenat ce kadai keta hidima umma datayimata maganar bikin sai kuka.




Hajiya saudat ce zaune falo tana duba  husnul Muslim,
Taji sallama tabada izinin shigowa  saitaga Hafeez ne ahahaha, Hafeez kaine yace Eh,hajiya,

Yadurkusa yagaidata  cikin ladabi  suka gaisa

Tace shiga yana cikin daki kullum kwance, tindashi bedaukar kaddara mai kyau KO marar kyau intazo mishi,

Hafeez yatashi yashiga dakin yanashiga ya iske Dr Ahmed kwance daki duk ya yamutse,

Gashi Dr Ahmed duk yatara suma,  ga kasumba tayimashi yawa, Haffez cikin mamaki yace Ahmed meke damunka,

Ka kuma haka kana kallan kanka Kuwa,

Dr Ahmed yatashi zaune cikin yanayi namar lafiya

Yace Hafeez yaushe kazo ne Hafeez yace bawaanan ta tambayeka ba meke damunka haka,

Dr Ahmed yace rashin saffeya, munrasa junanmu,
Hafeez yace. Mutuwa tayine,

Dr Ahmed yace A,a  Abbanta zaimata Aure da dan kanenshi,

Nan yagayamashi komai yanagama gayamashi tari yasarkskeshi, Haffez cemasa yake sannu Amma tari yaki lafawa dasauri Haffez yanufi wajen firjin daki yadauko masa, ruwa Amma yanashan ruwa, suka dawo yana Kara wani kakin sai jini,

Hafeez ya firgita  yace Ahmed!!!  Jini kezuba
Amma Ina Dr Ahmed yasuma,

Haffez dagudu yafita. Yakira hajiya,

           
               35


Hajiya tanashigowa taga halin da Ahmed yake ciki fashewa tayi da kuka  tace Haffez dauko mota, mutafi Asibiti dasauri  ya fiddo mota,
Ya ciccibi Ahmed hajiya tashiga suka nufi Asibiti,

 Suna shiga  Asibiti  Aka turo keken marar lafiya Aka dauki Dr Ahmed  Akashiga dashi
Hajiya da Hafeez sai zagaye suke hankalinsu tashe,

Kamar wajen minti 30

Doctor yafito Daga dakin daaksa Dr Ahmed  yace su same shi office,
               Bayan sun shiga sun zauna doctor yace ma hajiya Saudat kice mahaifiyar sa   tace Eh,
Shikadai gareni  doctor yakalli Hafeez, Kai kuma fa Hafeez yace Amininsa ne,

           36



Doctor yaja Numfashi yace gaskiya yana cikin damuwa sosai daf take ta taba zuciyarsa  Akwai. abinda yakeso, taredashi Asamomasa koma meye inbahakaba zai taba zuciyar sa Daganan kuma zuciyar na iya buguwa Ku rasashi,

Hajiya saudat tadafe Kai kome ta tuna tamike. Hafeez kaini gidan. Su safeeya inkasani

Hafeez yace safeeya tace Eh wadda Ahmed keso
Hafeez yace hajiya mezakiyo tace kaidai muje

Hafeez suka fito Daga office din doctor yaja mota suka nufi har unguwar su saffeyya,,

Har ciki suka shiga Hafeez yace tashiga yanan

Hajiya saudat tashiga tayi sallama. Meenat da umma suka Amsa ta domin sukadai ne zaune falo saffeya takoma yar cikin daki,

Suka Amsata  umma tace sannu ki shigo hajiya saudat tace yauwa tazauna bisa kujera

Umma tace Meenat tashi kidaukomata  ruwa,

Hajiya saudat tace A,a Alhmdlh,

Ummm tace saidai banganeba
Hajiya saudat tace mahaifiyar Ahmed ce  Umma tace Ahmed  domin bata ganeba,

Hajiya saudat tace wadda keson safeeya

Dama Alfarma nazo nema wajenku don Allah kutaimaka kuba Ahmed Aure saffeya shikadai gareni  Aruyuwata,

Umma taja numfashi tace gashi kuma Abba nasu benan kuma ni babu Abinda Zan iya cewa

Kuma yatafi office dawowar sa sai dare,


Karar mota sukaji umma tace kamar motarshi, to meya msidosh mantuwa yayi ne,
Toro kofar Akayi tare da sallama hajiya Saudat suka Amsa,
Dagowar fuskar dazatayi

Tamike zumbur yaya sule!!!!!

Abban su safeeya Colin tsananin firgita yace  saude!!!!


Tofa😳😳😳😳😳😳
  KUBIYONI


*lluv* *masoyana* 😘😘
[1/25, 2:51 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔
        Na

Hafsat ( Hafsy baby)

 

                37



Hajiya saudat Cikin tsaninin firgita tace yaya, sule!! Yace saude,
Kawai sai Hajiya saudat tafashe da kuka,

Umma Cikin mamaki take kallonsu  sunyi tsaye cirko cirko, Hajiya saudat Cikin kuka tace yaya sule dama kuna raye,
Kuka manta dani nashiga halin rayuwa,

Kullum tunanina haryazuwa yanzu inazanganku   Amma kunmantadani,


Cikin fushi tajuya zata fita,
Abba yace saude. Dawo don Allah zanfadamiki komai,

Cikii  kuka hajiys saudat tace mezaka fadaman yaya sule, kabarni natafi kawai nakarasa rayuwata haka tunda baka bukatata,


Cikin rararshin Abba yamaidota,
Daga waya yayi kawai yace kazo Nan gidana kaida matarka,


Kamar minti 10 Aka toro kyauren Akashigo,

Mustapha ne maihafin  Haidar tare da matarshi, sukashigo,
Yayi sallama, yazauna kujerar  kusada Abbansu Saffeya, mustapha cikin,

Mamaki yace Yaya kace muzo yanzu  kuma nasan bayanzu kakedawo ba kace mutafo,

Abba yace kalli can yanuna bangaren da Hajiya saudat kezaune,

                   38
                  Cikin  tsananin firgita mustapha cikin rawar murya yace saude... Tace yaya mustapha yace kece tace nice yaya mustapha, ba gizo idanuwanka sukemakaba,

Hajiya saudat ta mike dasauri domin sai yanzu tano dabaro Hafeez  zaune cikin mota,

Abba lafiya saude kika mike ne
Tace wadda yakawoni  ne namanta wallahi Kuma  Ga Ahmed kwance Asibiti,

Abba yace tokutashi mutafi Asibitin  mana domin bayari saude takara sakemashi,
Nan da umma sai Abba, sai kuma kawu mustapha da matarshi hajiya murja,suka tashi suka runguma sai Asibiti,

Duk Abinnan daake Meenat da safeeya basu saniba  domin Meenat Hajiya saude nazuwa tabar falon,

Tashiga ciki,

Tashin motocin kaawai sukaji taleko ta Meenat ta leko ta Window saitaga kawu mustapha da umma sai mamyn su Haidar sunshiga mota,

Saiwanna bakuwar tatazo tashiga itama,

Anbudemasu Gate sunfita,
Meenat meke faruwa ne,

Batada Amsar wannnan tambaya kawaintasaki labule. Takoma tazauna tana saureren dawowar su,

Abba sun isa Asibiti suka fito suka nufi dakin daaka kwantar da Dr Ahmed
Suka iskeshi har yanzu bacci yakeyi,
  Saiga Doctor yashigo yayi salllama domin yashigone yakara duba jikin. Dr Ahmed kowa yafarka,

Nan yadubashi yace karsu damu nan da one  hour sai farka insha Allah,
Sukace Allah yakaimu

Shikama Hafeez mamaki yake mail yahada Hajiyarsu Ahmed da iyayen safeeya, harsuka tafo tare Asibiti,
                  39
Bayan hour 1dakamar minti 10


Dr Ahmed ne yafara bude idonsa yaganshi bisa Gadon Asibiti sai yatunano Abinda yafaru dashi  bayan yagama bawa Hafeez labarin Abinda yafaru,

Yakara bude idonsa sai yaga Hajiya sa tare wasu baki yana Kara waiwaya yaga maihafin safeeya dakuma kingin bakuwar fuskokin dabasai kowaye ba,

Hajiya saudat tamatso wajen sa da sauri Ahmed kafarka yace nafarka Hajiya tace yanzu inayake maka ciwo yace zuciyata ke ciwo Amma basoisaba  tace zatabari Ahmed insha Allah,

Tace Ahmed  yau kukana yakare naga,yayyena, kaganasu,
Yaya sule, da yaya mustapha,
Tanuna maisu,




                40
BAYAN KWANA BIYU


DR Ahmed yaji sauki Alhmadullah, yayima hajiya Alkawalinan bazai sake kara sama Kanshi damuwa,

Falon  su safeeya ne Abba, kawu mustapha, umma,Hajiya saudat  Hajiya murja,  Haidar,  Dr Ahmed,
Saffeya, Meenat,


Abba yayi gyaran murya yace Alhmdullah Allah mungodemaka  Allah shine Abingodiya, A kodayaushe,
 Dayahadamu da kanwarmu, Wato saude, bayan dadewar damukayi bamu haduba,
Sai kwannan datazo nan gidan Akan tana Neman Alfarma Akan Aba Ahmed danta Aure saffeya, dasauri safeeya tadago fuskarta jin wannan batun jin Dr Ahmed dan uwanta ne,

Abba yace kafinan kowa zaishiga duhun jin nace saude kanwarmu ce ko  nida mustapha to saude kanwarmuce uwadaya ubadaya Daganan yabasu labari daga farko, har barowarsu kauye



                    41
            TUNA BAYA

Abba yadora yace bayan Baba yakawo makaranta bekara waiwayrmu.
Gashin malamin Azzulumine inkaje bara kadawo kasamo Abinchi kwacewa yake,
Dahaka mukai tahakuri domin bamu da makwancin kwana sainanan
Anahaka nida mustapha muka Fara shiga kasuwar central market munadago muna samun Abinchi dazamuchi muka daina bara,
Damunyi dako munchi Abinchi lokacin tashi yayi sai mutafi makaranatar da Akawomu, mu kwanta daan tashi dasafe munyi karatu, Antashi ma karanta sai mutafi, cikin kasuwa, ko makarantar marece daake zama bamu zuwa, Amma malamin besaniba domin shi babu ruwanshi,

Anahaka wata Rana nadauko ma wani  Alhaji kaya,   shinkanfa  yabude boot domin nasakamashi,

Ashe ya fiddo wata jakka baka.

Ya aje bayan nasa masa shinkafa yarufe boot din. Ban luraba  sai daya tada naga jikka Aje  nadauka nabishi Dagudu inbashi domim ya manta Amma nakasa cimmashi,

Nadauki jikka nan na nufi wajen mustapha nace mustapha kaga Alhajin danayima dako  yamanta jikkashi,

Mustapha ya Amsa yace mugani mustapha yana Amsa yabuda yagani yana budawa yaga dame dame kudi  yace yaya sule!!! Kudi ne ciki,

Naduba naga  kudine ciki nace rufe mustapha, nace taso muje,

Nan najashi muka nausa canciki inda babu mutane kuma nagaka babu mai hangenmu nayi rami na rufe jikkanan,

Kullum rokonake Allah yahadani dawannan mutumin.

              42


Kwatsam rannan ina yawo cikin kasuwa naga wannan mutumin yashiga wani shago naji rash har yafito, nabishi daga baya nace Alhaji,  yawaigo dominshi har yamanta dana taba daukarmasa kaya, yace yaakayi yaro nacemasa Alhaji kamantani ne,
Nine wadda yataba daukar maka shinkafaa har kamanta wata jikka,

Dasauri , hannu na cikin murna yace nataono yaro nacemasa muje nadaukomaka muka nufi har inda na binne jikka, nabashi,

Yabuda yaga kudin yadda suke haka suke, yarufe yace Alhmdlh nagode nagode. Yaro naji dadi,

Yasunanka nace masa sule yace suleman nagode, yace dan wane Gari nacemasa rimi, yace Kai daya ne nace nida kanena ne,

Daganan Alhaji Muhammad yafara taimakonmu nida mustapha, yabudeman shago cikin kasuwar central  market  muna saida Atamfofi,
Alhmdlh muna samu dganan Har Alhaji Muhammad yabanj jari  nakaina Aruyuwata bazan taba mantashi,
 Dagannan nace mustapha yafara zuwa makanta yabarni shagon
Daganan akayimasa cukun cukun takardun primary kawai yatafi secondary,
Yanabarina shago nikuma,

Munata sanaarmu cikin rufin Asiri, har yakammalaa
Yatafi FCE can suaka hadu da murja suka Fara soyaya ,
Akace yaturo iyeyensa Alhaji Muhammad yayi mana tsaye har Akayi bikinsa,

Nan muka yanke shawarar tafiya dauko saude  munje mun isa lafiya Amma bamu Bari kowa yasan dazuwanmu ba sai Abokina Ilu nan yake gayaman bayan tafiyarmu Anyi bikin  saude da Iro,
Subar garimamn
Nan ranmu yabaci kowajen maifinmu bamuje ba domin munsa bamu gabanshi Azzulumar matarshi tarabamu dashi,


Saidai mustapha yayi shekara 5 da Aure sannan nayi na Auri Khadeeja sannan An haifi haidar yana shekara 4 tanazuwa sayayea shagona,

Nanma Alhaji Muhammad yayimani  tsaye akayi bikina  Aruyuwata bazan manta Alhaji Muhammad ba Allah yajinkanshi,

Khadeeja haihuwarta na farko ta haifi hassana da hussaina, wato saffeya da Ameena,
Daganan haihuwarta ta tsaysmata, shima mustapha haka,

Daganan muka bude company mustapha yana zuwa kasashen waje sari,

                 43

Muka sayi fili muka gina gidajennan nida mustapha,
Tuntashi safeeya da Haidar suka shaku dgaann mukayi Alkawrin hadasu Aure,
  Falon kowa yayi shiru kakeji,
  Daganan Hajiya saudat ta Dora itama harysxuwa yanzu,
Dr Ahmed halin dayashiga
Sanadiyyar safeeya,
Dr Ahmed yace hajiya  bantari Numfashi kiba tunda  haka Akayi Abba sunyi Alkawsrin Sure hada Aure  itada  Haidar Nina Hakura kidaina  tunanin haka insha Allah Zan cire damuwa ,
Inayimusu fatan Alkairi,
Ya mike yafita, daga falo
Domin wani Abu yaji ynaamasa ciwo,
       


 
              44

Safeeya itama tashi tayi tashige daki tana Kuka,


Tofa Rana bata karya  yau daurin Auren safeeya.

Hajiya saudat tashigo  daki ta iskeshi kwance tace  Ahmed bazakaje daurin Auren ba  kuma kace kafidda damuwar komai,

Yace Hajiya namanta  ne Bari natashi natafi,
Tace yauwa dan Albarka,

Dr Ahmed yatashi  yashiga toilet ya shirya bayan yashirya yakira Hafeez yace suzo suje sauri Auren saffeya,
Bayan ya I so suka nufi masallachi  unguwar su safeeya inda   Ake daurin Auren,

Suka iske Anfara taruwa  Ana niyyar daurawa,

Dr Ahmed kasa daurewa yayi, yafito daga masallachi nin
Yanufi baya yazauna kasa sai Kuka share share Hafeez yaga fitar yaviyo bayanshi yana  rarrshin sanarwa daakayi cikin lasifika!! Shine ya tsaida numfashi Dr Ahmed cak!!!

Tofa meya jawo haka😳😳


Muje zuwa

Luv you masoyana😘😘
[1/25, 7:56 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON SO💔
          Na
Hafsat (Hapsy baby)

         45



Cak numfashi Dr Ahmed yatsaya jin Abinda me lasifika yace.

Andaura Aure. Safeeya suleman tare da Angonta Ahmed Ibrahim, Akan sadaki, 50k

Zumbur Ahmed yamike Hafeez  ma cikin kidemawa, yace Ahmed kaji Abinda  naji Dr Ahmed yace nadauka nikadai nace nazauce Akan saffeya,

Hafeez yace taso muje, ko mantuwa marokin yayi ne,

Dr Ahmed  yakkabe rigarshi suka nufi wajen daurin Auren,

Suna fitowa nan Dr Ahmed yaga dangin maihafinshi,

Yaga har da Abonkasa wadda suke koyawa  A ummaru musa university,
Sun nufoshi sunata yimasa Allah sa Alkairi,
Dr Ahmed Binsu kawai yake da ido domin tsabar rudewa,

Haidar yaga yanufo wurin shi, yaya Ahmed inayi maka fatan Alkairi Allah yabaku zaman,
Ahmed besan lokacin da wasu hawaye suka zubomasa saboda ya fidda rai daga zai Auri saffeya,

Haffez yace Kuka kuma Abokina,

"Dr Ahmed yace na murna ne,Abokina, bantaba tunanin Aure saffeya tare daniba tuni " nafiida, rai daga hakan




Abangaren safeeya Kuwa,  Agogo ta kalla taga 11:30 Am
Fashewa tayi da Kuka tace yanzu harnazama matar Haidar ba Dr Ahmed ba,

Wayyo ni Allah, na
Meenat dake gefenta tace sai kitashi kinsan Aikin gama yagama, yanzu kinzama matar Wani sai kifidda, shi daga cikin ranki,

Gidan kawu mustapha falonshi Abba ne tare da   Hajiya saudat sai haidar sai Ahmed,
Abba yace zakaji Abu kamar mafarki ko Ahmed,
Jin Andaura Aurenka da saffeya ba daura Mata da   Haidar,ba

Abinda yafarune kingi kwana biyu Adaura Auren Haidar yasameni Akan yanason Afasa dashi Adaura dakai,
Tunda kaima nagidane kuma safeeya tafi sonka,
Naki yarda da hakan kawai sai yafasheman da Kuka sai Na Aminche,

' nadauki waya kawai nakira mustapha nace yazo inasan ganinshi yazo nacema haidar ya maimaita Abinda yace yakuma maimaita,
Nace meyasa yake fadin haka, yace saboda ya Lura safeeya tana matukar kaunarka kaima kanasonta,

Kuma  duk Abinda kaso ma dan uwakan musulmi ladanka yana wajen Allah, shiyayi jihadi yabarma Ka safeeya, shikuma Allah yazabamasa mafi Alkairi,
Amma yace kar Afadimaka sai kaje daurin Auren saikaji,
Kaji yadda Akayi,

Dr Ahmed yajuyo wajen hajiya Saudat yakalleta, tace Hakane Ahmed Andaura Aurenka da safeeya, ance Karna fadamaka, kuma Anyi sanarwa gidan radio kaine bakajin radion da kuma Karin kana cikin damuwa,shiyasa babu Abinda zakacema haidar sai godiya,
Dr Ahmed yajuyo wajen  Haidar ya rungumeshi nagode nagode. Dan uwana Allah yabar zumunchi, kawai yafashe da Kuka, Haidar yace babu komai yaya Ahmed, karka damu.



Saffeyya kuma sai fama Ake da ita tatashi tayi wanka Amma tace  bazatayi ba
Umma ce tashigo dakin fusace waike wane irin yariyane, wallahi Zan daka miki shegen duka  yanzu koki tashi kishirya, yanzu,  tashi  kishiga toilet din gabana,
Safeeya cikin Kuka tatashi ta shiga toilet tayi wanka tafito,

 Meenat tahau shiryata itada wasu friends dinsu wadda sukazo tasa wani coddles, pink And pupurle,

Masha Allah  Allah Abin godiya safeeya tayi kyau,

Nan wata kanwar mamansu taja xuwa. Dakin Abba domin bakwana suka iske umma da Abba zaune  Auntysadeeya. Kanwar umma tace ga safeeya,
Nan tazo muku bakwana,
Abba yayi gyaraa murya yace safeeya tace Na' am Abba cikin sheshekar Kuka,
Yace Aure ibadane da dukkan wata ya mace

Kiyima mujinki biyayah saidai iyawarki inayi Bari nabari Aljanarki tana karkashinsa,
Komai yace kibari kibari
Nan Umma tadora tata itama
Bayan sungama Abba Allah  yabda sa'ar shiga gidan muji.

Aunty sadeeya taakmo hannuta domin motici sun Akejira,

Safeeya tajirce ita batazuwa Akyaleta wajen ummata sai kuka,
Umma itama daurewa kawai tayi,dakayar Akafita da safeeya.
Bayam sunfita Abba kefadama umma da Dr Ahmed Akadaura bada haidar, yafada duk yadda Akayi, umma tayi mamaki Amma tace Ikon Allah kenan.

Bayan Akai safeeya gidanta dake Dutsin safe low cost,
Bayyana kyau gidan yayi kadan na bayyanashi cikin yar mitsitsiyae wayata,
Amma nabaku Gari,

Dakyar Aka banbare Meenat da saffeya Daga jikin juna domin safeeya tace babu inda zata, tabarmata,
Dakyar Aka kwaceta,

Kowa yatafi   yabar safeeya  ita kadai, sai kuka take,

Ahmed kuma sai zanzarar Hafeez yake yazo yakaishi  gidanshi yake. Shikuma yana ta tsokanarshi,

Dakayar yajashi suka tafi..

Luv you masoyana😘😘😘
[1/26, 3:30 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON  SO💔
        Na
 Hafsat ( Hapsy baby)



46



Safeeya tanajin karar mota. Dasauri tatashi ta kulle  dakin  takoma ta kwanta domin kosan ganin  Haidar din( Anufinta ba haidar Aka daura Mata Aure dashi,


Tafashe dakuka yanzu nazama matar Haidar ba Dr Ahmed,

Nantayi sauri istigafari domin tace Astagafurallah,

Allah yafeman na Ambaci wani  dakuma Aure bisa kaina,

Tadora pillow bisa kunneta domin karma ya isheta da hayaniya


Shikam Dr Ahmed Suna shigowa dakin safeeya yazarce  Amma me sai ya iskeshi kulle,
Murmushi kawai yayi yadawo wajen Hafeez dake  falo yazauna,
Yace Abokina kaga ta kulle kofar tadauka Haidar domin.
Haryanxu baasanarmata dakowa Aka daura Auren ba,
 Hafeez yace yanzu yazakayi to???


Dr Ahmed yace kyaleta nima zankyaleta kamar 1 week sannan na bayyana Mata kaina,

Hafeez yayi murmushi yace shikenan nibari natafi ko
Yarako sa har Bakin Get,
Sannan yakoma ciki yashuri ledar dayashigo da ita yanufi dakinsa,

Itakama haka tayi bacci kudundune Kamar  wadda zaasace,


 Kiran sallar Asuba yatadata  domin Akwai masallachi kusada dasu,

Anatada sallah tatashi tayo Alwalla,

Lokacin datake Alwalla shima yatashi domin tafiya masallachi,
Yaji motsin ruwa, yasan tatashi shima masallachi yanufa kawai,


                  47

Bayan ta idar da sallah ne komatayi ta kwanta, bacci yakomata sabo,

Bata farka ba sai wajen 11 am
 Tana farkawa taga 11 tayi    dasauri taduro Daga bisa gado, tace wai nadade Ina bacci Ashe,

Tanufi toilet tayi brush,

Tanufi Hanyar waje domin gano kitchen domin Cikinta yafara kiran,

Ciroma,tea kawai tahada mai kauri  tadawo  falo tazauana,

Hango wata fara takarda tayi Bisa  table din tsakiyar falo din tadauko ta tabuda taga,Antubuta,


```My``` ```Wife``` ```Good``` ```Morning ```

```nadan``````Fita``` ```Sorry ``````Luv``````you

   

Tsoki  saffeya kawai tayi tace Kama ka dawo bana raayin ganinka Kama,

Nan tagama Abinda zatayi tashigewarwata daki domin bata raayin kallon fuskarshima, nace uhumm safeeya duk A cikin rashin Sani ne,

Shikam Dr Ahmed yana dawowa Daga massalaci shima yadan kwanta,

Wajen Goma yafarka yatafi wajen Hafeez inda yasauka,

                48

Abuna yanata tafiya safeeya batasan haryanzu  Dr Ahmed ne mijinta kuma Suna waya Dr Meenat lafiya lau, bata taba sanar da itah
Domin Dr Ahmed yacema Meenat kartasake tafadamata shine mijinta hartaganshin takanta,

Yau safeeya tatashi cikin murna domin sunyi waya da Meenat jiya yau tanan tafe,

Tashi tayi taga Akwai Abinda zatayimata,
Tanufi kitchen,
Tabuda firji taga Akwai kaza da naman rago,
Kaza kawai tadauka zatayi Mata farfesunta,
Bayan tagama tayimata jallof rice taji kayan hadi sai  tashin Kamshi take,
Tahadamata juice pine apple And coconut
Tahadasu bisa table A  tanufi dakinta dominntayi. Wanka kafin taiso

Bayan tagama wanka tafito tayi sallar Azahar domin lokacin yayi tagama tanufi  mirror domin shiryawa
Tanagamawa, tafiido wani paper lace blue And yellow kyau da saffeya tayi baa magana,
Tafito falo domin jiran Meenat bada jimawaba saigata tashigo suka rungume juna cikin murna,
Nan safeeya taje suje  falo domin cin Abinchi data girka mata,

Suna zaune falo Suna firar su ta zumunchi,
Toro kyauren Akayi tare da sallama,
Saffeya tadago daga cin Abinchi datake tadago fuskarta kawai taga Dr Ahmed A razane Abinchi datake yadawo.....


 Luv you masoyana😘😘
[1/26, 7:58 PM] Hafsat ( Hafsy Baby): 💔CIWON  SO💔
           Na

Hafsat (Hapsy baby)

              49&50
   

            LAST PAGE






Cikin kwarewa tamike sister
Kinaganin  Abinda nake gani kodai idanuwana sufara Gizone soyaya zata Sani Hauka Dr Ahmed yanayimana Gizo, tafara kuka,   Meenat tataso Daga inda  take tadafata tace sister Dr Ahmed bagizo yakemakiba shine mijinki wadda Aka daura muku Aure dashi, saffeya tace bafa Haukacewa nayi ba. Sister da  bacin da  yaya haidar  Aka daura shine yanzu zaki fadaman Dr Ahmed aka daura Aure na,


_Meenat_ _tayi_ _Dariya_  _tace_ _wallahi_ _tallahi_  _sister_ _Dr_ _Ahmed_ _Shine_ _mijinki_  _wadda_ _Aka_ _Daura_ _muku_ _Aure_ _dashi_




Taso muje kiji yadda Akayi.
Shikam Dr Ahmed yayi tsaye bakin kofa sai murmushi yake,

Meenat tajawo hannu saffeya tace yadda Abu yafaru, Kuwa,tagayamata duk yadda Akayi, tana gamawa
Safeeya tafashe dakuka tatashi dagudu tashige daki,
Tafada bisa gado.

Dr Ahmed yacema Meenat Bari nabita Meenat tasabi  jikka da gyalenta tace nayi nan yaya Ahmed,
Sai Anjimanku

.  dr Ahmedyatura kofar dakin saffeya yahau bisa gadon datake,
Yace safeeya!! Amma taki dagowa sai Kuka take,
Yasa Hannu sa yajawo tafafa bisa jikinsa saffeya kukan mekeke kedayakamata kiyi murna kiyi farinciki Amma bazaki ta Kuka Haba my  heart beat pls Adaina kukan nahakanan,
Mugodema Allah daya cikamana burinmu, munzama mata da miji  nidake,
Cikin Ajiyar zuciya safeeya tayi  kamar yarinyar Goyo cikin shagwaba tace to meyasa Baa fadaman tun Ranar ba,
Dr Ahmed yace ninace kar asanardake, sainashigo kuma nashigo Ranar na iske ki kulle kofa nikuma nace sai nakara janki bazan bayyana Hakan garekiba  sai yau, sai gashi kuma nayi sa' a Meenat tazo kinfito falo, kuna zaune,
 Safeeya Kara tura kanta tayi kirjin Dr Ahmed Ahmed shima Dr Ahmed yakara rungumeta Kamar zaa kwace ta ganin zai wuce  Gona da iri safeeya tace kai sir munbar sister A falo fa,
Dr Ahmed yace tatafi Ai,
Cikin shwagaba tahau dirara kafufuwa. Meyasa tatafi bata fadamata ba,


Dr Ahmed yajawota zokiji wata magana tafaada bisa jikinsa,

Daganan bacci yadaukesu Har zuwa wajen la' asar suka farka sukayi sallah tare,


Can nahango saffeya tare da Ahmed suna girki,  Acikin kitchen, Ana girki Ana love,

Bayan sungama suka zubo cikin plate daya wannnan yaba wannanan harsukaa gama,

Lokacin sallar magariba tayi Dr Ahmed yanufi masallachi yacema safeeya zai Kai isha' I zai je wajen  Hafeez,
Safeeya bayanan ta idar da sallah tashiga ta silalo wani wanka,

Tazauna gaban mirror tadinga lindar jiki Kamar zata canja fata,

 Tana cikin lindar jiki tatashi ta maida isha' I

Tagama tadawo saida tafi minti 30 tana lindar fuska sannan, tatashi tajawo  wata Atamfa   pink And blue tasa,masha Allah saffeya tayi kyau,

Tadawo falo tazauna tajiran Hasken kalbinta,

Batayi minti goma dazama sai gashi yadawo tanajin horn din motar takara gyara zama, can ya shigo,
Yace wow Masha Allah my heart beat kinyi  kyauyabata kiss Akumatu. Yazauna kusada ita suka kalli labarai

 


Karfe Tara nayi yakashe kallon yace suje daki lokacin bacci yayi yasabi saffeya kamar jariyaya,suka nufi dakinshi,

Yana direta yace inazuwa yafita minti kadan yadawo da plate da bakar Leda yacemata My princess taso muci ko ya fiddo wata dankwaleliyar kaxa
Yayagi cinya🍗yasakama saffeya baki nan dai suka ci kadan suka tashi,
Saffeya tamike tace Sir sai dasafe kada Kai kawai yace OK night,

Safeeya tanufi dakinta,  tacire kayanta na bacci

Tahaye Gado tayi Addu' a kwanciya bacci  can bacci yafara daukata taji An kunna lantarki Amma bata motsaba can taji Ance safeeya  cikin Almun bacci tafarka Taga Dr Ahmed tsaye,
Yace tashi muyi sallah  cikin bacci tace nayi sallah nifa, yace bawannan wadda ma'aurata keyi,
Tashi nida Alwallata tashi kiyo taki inajaranki
Safeeya tadiro daga bisa Gado tanufi kewayen tayo Alwalla,

Tafito suka tadda sallah bayan sungama sukayi Addu' Allah yabasu zaman  safeeya nahar Abada
Dr Ahmed Yayi ma safeeya wasu tambayoyi yaji  ta Amsa masa,
Nan tafaera gamma tace
Sir nafara jin bacci yace OK babu matsala mu kwanta  KO, face nan zaka kwana ne yace Eh, kokar nakwana 
Dakin matata face A a nidai Vance ba yajawo musu bargo suka lullube, can Dr Ahmed ya rungume  safeeya yafara, kiss  Daganan komai
Yacanza
Nima Daganan najawo musu kyaure nafito  Falo
Can nafara gyangyadi  Naji karar saffeya firgice natashi nanufi  dakin  saffeya,
Amma magen dasuke kiwo ita tamaidoni kusunssani   da tsoron mage sosai
Shiyasa suka a

jeta


Dagudu nadawo falo  nahaye kujera  can nakarajin ihun safeeya tana kiran  Umma da Meenat, Har Abba  nidai  babu halin ceto domin ganin magenan

Tun inajin kuka safeeya har bacci yadaukeni ceke da tsoron mage☹☹



Washe Gari

Safeeya ce tasauko Gado Anhakali domin wani zafi datakeji tanufi toilet domin hada ruwan dumi tayi wanka

Dr Ahmed yana lalubawa  yaji ba  safeeya sai yasaurara  yaji karar ruwa toilet dasauri yasakko yanufi toilet zanbishi ya wurgma man harara nadawo da sauri na nufi falo,
Can naji dariyarsu  firgit nafarka naga wai harsun shirya sunfito,
Falo Dr Ahmed yaja Hannu safeeya suka  zauna  mezakici my dear cikin shawgaba tace  tea kadai Zan sha,yace    Angma ranki yadade,




       
Soyaya tsakanin safeeya da Dr Ahmed sai Abinda yakaru suke.kowa yasan yafaranta makowa,

Yauma zaune take tanajiranshi falo zasuje gida  zasuje rimi kauyen su Abbansu wato rimi,
Duka zasu tafi,

Bayanan Dr Ahmed yashirya suka runguduma suka tafi Gidan su saffeyya domin can zaahadu,

Suna xuwa suka iske harsu Abba sun shirya, kawai suma mota, suka koma,

Safeeya gaba sai Dr Ahmed dake Jan mota sai Meenat da Haidar baya,
Can  kuma motar guda
Umma sai Abba sai kawu mustapha da mamy,
Sai Hajiya saudat,

Nan suka runguda sai rimi
Minti talatin yakaisu har kofar gidansu Abba,
Suka rufe mota,suka shiga shiga,
Har ciki suka iske wata tsohuwa zaune makauniya, zaure da sauri Abba yace Inna, cikin laluba tace waye   yace sule ne, tare da mustapha da saude

Cikin firgita tace sule Ashe kuna Raye,Abba yace munan da ranmu, Ade tafashe da kuka kuyafeni nayi kukskuren Arayuwata
Allah yajikan malam inama da ranshi
Abba yace Baba yarasu tace  tace Allah Yayi masa rasuwa Asanadiyar hawan jini bayan Asirin danayimashi yakare yafara tunaniku dgn yakamu da cuta har mutu yana maganar Ku,
Nikuma dama bokace duk Randa yamutu Zan makance,
Abba sukace Allah yajikan Baba yayimashi Rahma,
Cikin kuka Ade tace Ameen nacuci kaina,
Nan Abba yadubi Gidan yadda yaruguje yalalace, nan yace dayadawo sai dawo da magina daga katsina domin su gyara gidann


Bayan wata shida


Dr Ahmed shida safeeya sunfito daga Asibiti yakai safeeya Awon cikinta dan wata biyar,
Kawai yaga wata Mata tatsreshi bawan Allah Ataimakaman da sadaqar Abinda  Zan siyi magani
Dr Ahmed yazaro nari biyar ybata  cikin kyarma ta Amsa  nagode yace babu damuwa
Wadda yaba sadaqar cikin  rawar murya tace  Ahmed...
Yadawo yace vaiwar Allah inakikasanni,
Tace Basma!! Ce
Dr Ahmed yace Basma badai wadda nasaniba tace itace kayafeman Ahmed nayaudareka Arayuwa saboda kwadayi,
Gashi babu inda yakaini Ashe Mahmud manemin Mata dan Giya,

Bayan Auren mu dashi da shekara biyu ya kwanta ciwo Aka kaishi Asibiti Ashe cutar Aids gareshi badaidai Asibiti ya mutu  nima Aka Aunani Akaga inadata
Daganan komai nawa yakare gashi bahaihudashi balle nassmu gadonshi, shine nake fitowa nakesamun na magani,
Dr Ahmed ya girgiza  kawai yace Allah sawakka yaja Hannun saffeya sukabar wajen,

Bayan wata ukku

Safeeya naga tatafo falo da katon ciki rikeda da apple A Hannu Amma tayi tayi taka kafarta taki takuwa dasauri tafara  kwadama Dr Ahmed Kira, honey
Dasauri Dr Ahmed yafito daga dakin yana ganin halin datake yacuccibeta kamar jariyaya  sai mota  yasata yadawo yadauki Akwatin dasuke  sa kayan baby
Sai Asibiti dakin haihuwa da sauri Aka  Amshi safeeya  sai daki haihuwa,
Dr Ahmed yna zarya can yaji kukan jaririya saiga  nurse tafito tace inatayka murna Ansamu baby girl Dr Ahmed cikin murna yace Alhmdlh

Yadauki waya yakira hajeeya saudat  da Umma
Nandanan suka zo

Bayan Angyara jaririya da mahaifiyar ta Akabasu sallama,
Babu inda Aka zarce sai Gidan saffeya Hajiya saudat tace zata zauna ta kula da diyarta

Agurguje

Ranar Suna

Anyi suna Alhmdlh taron suna yakayatr dakowa
Diya taci sunan  Hajiya saudat Amma zaadinga kiranta   Bunayya
Nan Meenat kesanaer DA saffeya sun daidaita  da yaya Haidar
Dasun dawo bautar kasa zaayi bikin  dayake kingin sati biyu tafiyar Amma Dr Ahmed yace   zaayi yadda sukayitasu  cikin garinsu,

Haffez shima Yayi Auren yanazaune kusada DA Dr Ahmed

Dr Ahmed ya shigo dakin safeeya ya iske Bunayya sai kuka take  safeeya tana rarshinta dasauri yce meakayimatane safeeya tace rigima Dr Ahmed ya Am she ta yarungume yajawo saffeya yarungume yace  I luv you my mu wife tace iluv you my husband


Alhmdullah Anan nakawo karshen CIWON SO  SAI ATARENI A SABON LITTAFINA ..

ILUV YOU ALL MASOYANA BANDA KAMAR KU. ARAYUWATA.😘😘😘


Godiya ta mussam gareki

Mrs Lameedo Allah yabar zumunchi


Masoyana sai munhade sabon book Dina mai suna ....😜😜
adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *