Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, December 23, 2019

Ni Da Aminiyata! complete hausa novel

adsense here

Ni Da Aminiyata! complete hausa novel

[12/19, 7:24 PM] mrs bilkisu: 1~October~2016

🔶🔸NI  DA K'AWATA🔹🔷


NA BILLKISA IBRAHIM💕




🔷🔹1⃣🔸🔶


BISMILLAHIRRAH MANIRRAHIM
Da sunan ALLAH mai rahma mai jink'ai, ya ALLAH kabani ikon fad'in abinda zai amfani Al'ummarka, ka tsarkake harshena daga fad'ar abinda zai cutar da Al'ummarka. Amin ya "RABBI".

Assalamu alaikum, ina mai farin cikin sake had'uwa daku asabon littafina, akaro na 4, ina godiya ga d'umbin masoyana aduk inda suke, "UBANGIJI ALLAH" yabar k'auna. Nagode🙏🏻

Zanyi amfani da wannan dama, domin taya d'umbin Al'ummar MUSILMI shiga sabuwar shekarar musulinci, ALLAH ya albarkacemu da rahamarsa.
    🙋HAPPY NEW YEAR🙋



..........'Yammata biyune ke tafiya, cikin nutsuwa, jikinsu sanye da kayan makaranta, (uniform) pink d'in wando da farar riga, sai farin hijjab daya tsaya musu iya k'ugu, dan baikai d'uwawunsuba, bayansu goye da jakar makarantarsu (school bag).
       "Sukaja birki abakin titin da d'umbin  d'alibai ke tsaiy tsaye suna jiran motar makaranta,wash ALLAH!!!, d'aya daga cikin 'yammatan ta fad'a.
 D'ayar ta bita da kallon mamaki, kai fareeda badai gajiyaba???
     "Wadda aka kira fareeda tad'anja tsaki wlhy kuwa sopy nagaji.
Sopy tai dariya nikam bansan randa zaki zama jarumaba fareeda, ke komai kin gaji sai kace mai yaron ciki??
       "Fareeda ta harari sopy, "k" ki kaimin cikin ko??
Gaba d'aya suka tuntsure da dariya harda tafawa,, sopy tace"ina ni ina yimiki ciki rufani ki sayani,, suka kuma tuntsurewa da dariya.
 Tsayuwar wata bak'ar motace ta tsayar musu da dariyar,suka k'urawa motar idanu, da alama sunsan mai ita, ko kuma suna son sani.

Wani farin saurayi mai d'an jiki yafito yana murmushi, idonsa akan 'yammatan, yak'araso da sallama, suka amsa cikin sakin fuska, suka gaisheshi, sopy ta d'ora da fad'in habibina daga ina?? Da wannan farar safiyar ga sanyi??
     Ya shafa sumar kansa, yana fad'in gimbiyatace ta fito dani ko fareeda??
Fareeda tai 'yar dariya mai kama da yak'e,, tace''hakane.
Saurayin yayi d'an murmushi to kuzo mutafi karku makara, dan wannan motar makarantar taku saiku kai k'arfe takwas baku tafiba, yafad'a yana karb'ar school bag d'in sopy.
                     "Sopy ta tab'a fareeda K'AWATA tunanin mi kikeyi ne??
Fareeda taja ajiyar zuciya bakomai mikika gani???? Sopy tace''ban yardaba fad'a min gsky!!
Kunga kumuje sai ayi wannan magar a mota, saurayin yafad'a yana nufar motar.

Suka bishi abaya, bayan sun shiga motar, yaja suka tafi,, sopy tadage sai fareeda tafad'a mata damuwarta, ita kuma fareeda tadage akan babu abinda ke damunta.
    Saurayin yay dariya nikam tunda nake arayuwata bantab'a ganin k'awance irin nakuba, mai cike da k'auna da yarda, dakuma aminci, wai idan kun tashi aure yaza ayine??
      "Sopy ta kalli fareeda, my sister kinji wani zance,, aii mu insha ALLAH agari d'aya zamuyi aure ko?? Fareeda tace" insha ALLAH.
Tofa saurayin yafad'a, to ALLAH yacika muku burinku,, amma aii har yanzu bamusan gwanin K'AWAR tamuba??
Wlhy habibina nima kullum damuwata kenan,, bani da wani buri bayan naga mijin k'awata, tunda ni nakama nawa tafad'a tana kallon saurayin,, shima ya kalleta yay Murmushi, fareda yakamata ki tsaida gwani gashi har munkusa k'are makaranta.

Fareeda tad'an ja tsaki mara sauti, azuciyarta tace,, haba K'AWATA dama kin daina zumud'in ganin gwanina,, dan ganin mijin dazan aura bak'aramin tashin hankali bane agareki,, dan saurayin dakikeso da k'yauna shine wanda nake burin yazama mijina kota halin k'k'a😳😳 tofa.
Amma afili saitace karku damu gwanina yakusa bayyana insha ALLAHU.
   "To ALLAH ya yarda cewar sopy"

A bakin get d'in makarantar ya ajiyesu, suka tsaya shida sopy suna sallam, yayinda fareeda tai gaba zuciyarta na zafi saboda kishi.
Bayan yatafi sopy tak'araso inda fareeda ke tsaye fuska a d'aure,, sopy tabita da kallo dan son gano matsalar K'AWARTATA,, amma sai fareeda tai gaba, tabar sopy a tsaye tana kallonta.
       "Sopy tabita abaya, tana mai mamakin duk sanda suke tareda ABDUL sai fareeda taita fushi ko me yasa hakan???
  Zuciyarta tace k'ila itama tana sonsane, kobatason tarayyarku,, tai saurin cewa kai A'a fareeda bahaka takeba,, domin na yarda da fareeda d'ari bisa d'ari,, nayarda da ita kamar yanda na yarda da kaina,, shaid'an bazan yarda da hud'ubarkaba, balle har ka haddasa rashin yarda tsakanina da K'AWATA, abin sona da k'aunata,, dan bayan iyayena da 'yan uwana, babu wanda nake k'auna kamar fareeda da Abdul, mutanan nan biyu sunada matuk'ar muhimmanci arayuwata fiye da tunanin mai hankali.

Turk'ashi lallai akwai matsala,, shin yazata kasance  ga fareeda da safiyya,, shin miyema dangar takar fareeda da safiyya ne?? mizai faru ga wad'annan k'awaye biyu?? ga fareeda taci  burin auren saurayin k'awarta aminiyarta,, wanda kuma k'awartata tafi so da k'auna, gashi yakai kud'in aurenta,, shin burin fareeda zai cika?? Idan safiyya tagano fareeda nason ABDUL yaza ayine???
 Nice kad'ai mai baku wannan amsar,, kubiyoni dominjin gundarin labarin ""NI  DA K'AWATA"" yananan zuwa nan bada dad'ewaba, takuce dai mai sonku da k'aunarku BILLKISA IBRAHIM.. nagode🙏🏻..............✍🏽



💕Bily💕
💕💕Mrs Abdus'salam💕💕💕?
 💕 I LOVE U MY FAN's   💕💕
                                              💕
[12/19, 7:24 PM] mrs bilkisu: 2~October ~2016

🔷🔹NI  DA K'AWATA🔹🔷


NA BILKISA IBRAHIM💕




🔶🔸2⃣🔸🔶

ASALIN LABARIN ............WACECE SAFIYYA???? SAFIYYA IBRAHIM KABEER shine cikakken sunanta , malam ibrahim shine mahaifinta, cikakken haifaffen kano ne, a unguwar rijiyal lemo,, kowa dai yasan rijiyar lemo unguwar talakawace irinmu.
     "Dan haka malam ibrahim talakane tib'is irin wanda sai annemo na gobe aci, sai dai malam ibrahim yanada wadatar zuci, dan mutumne mai taka tsantsan da tsantseni, matarsa d'aya hajara wadda suke kira da inna, itama mace mai hak'uri da kawaici, yaransu uku duk mata, Nafisa itace babba tayi aure harda yara biyu, dan daga aji uku na secondry aka cireta akai mata aure,, sai hauwa'u itamadai tayi aure kamar 'yar uwarta itama tana aji uku akai mata aure, yanzu tanada yarinya d'aya dan ko tafiyama bata farayiba; suduka suna aure anan cikin garin kano, sai auta safiyya wadda yanzu take (s,s,3) a wata secondary ta 'yammata, itamadai malam ibrahim yayi niyyar cireta yay mata aure amma sai uncle kabeer wani k'aninsa yahana, malam ibrahim yace" to shikam gsky bashida k'arfin rik'e ragamar karatunta, uncle kabeer yace" babu damuwa shizai d'auki nauyin karatunta dukda shima bawani k'arfine dashiba, amma yana aiki dan yayi karatu har zuwa degree.
Wanna nan shine dalilin cigaban karatun safiyya 'yar gatan uncle kabeer.  
      " gidan malam ibrahim ana cikin hali na talauci da fatara,amma wannan baisa 'ya'yansa sun lalaceba, saboda tarbiyyar dasuka samu a wajen inna da babansu,  gasu ALLAH yabasu kwakwalwar karatu sunada k'ok'ari a makaranta, dan safiyya tuntana primary school  take d'aukar na 1, har yanzu datake a secondary.
        "" safiyya bak'ace saidai bak'inta mai k'yawune, irin wanda idan ka kalla saika sake kallo d'innan, tanada k'yau am ma bamai tsananiba,  sai dai tanada manyan idanu dara dara wad'anda saudayawa susuke fara jan hankalin maza gareta,, gata tanada jiki mai k'yau irin wanda akecema karuwan jiki.

Fareeda 'yar anguwar su sopy ce dan gida biyarne tsakaninsu, itamadai iyayenta talawane dan babanta abokin malam ibrahim ne, su hud'u iyayensu suka haifa maza biyu mata biyu itama itace auta,, fareeda k'yak'yk'awace fara tas, dan tanada k'yau na d'aukar hankali,, fareeda k'awar safiyyace tun suna yara, dan ayanda najima rana d'aya aka haifesu,, k'awancensu yanada matuk'ar dank'o, dan tare yake da tsantsar so da k' auna dakuma yarda,, koda yaushe suna tare inbasa gidansu sopy to suna gidansu fareeda,, masu karatu amintakacefa mai tsantsar karfi ga wad'annan matasan 'yammata.
          "Koda yaushe suna  tare, tare a ka sakasu makaranta, ko d'inki tare ake musu iri d'aya kuma,, sai dai halin fareeda dana safiyya sun bambanta, safiyya tana da hak'uri da zuciya dan idan tayi fushi fareeda ce kawai ke iya shawo kanta kokuma uncle kabeer, Dan shine ma yasa mata suna sopy,, takan dad'e batayi fushiba dan sai ankaita mak'ura sannan.
                     Fareeda kam tanada tsiywa dan bata barin saita kwana,, soda yawa itace ke jawo musu fad'a gata batada k'arfi sai dai safiyya tashigar mata fad'an, kunsan masu zuciya akwai k'arfin tsiya,, fareeda tanada son nuna ita watace dan tanada kwad'ayi damma sopy tana sakata a hanya.

Tafiyarsu tafara samun gar gada ne alokacin da Abdul yashigo rayuwar safiyya,, shima d'an anguwarsu ne,, amma abayan layinsu yake,,babanshi yanada rufin asiri dan gsky yafi iyayensu safiyya kud'i.
         "Gidan su Abdul gidane na mata uku, da tarin yara dasuka kai adadin ashirin zuwa sama, Abdul shine na 6 a gidansu,, yayi karatu har zuwa (N,C,E)Sai dai Abdul irin samarinnan ne 'yan k'arya dason nuna burga.
Sun had'u da safiyya awani yammacin ranar talata, lokacin sun dawo daga islamiyya itada fareeda,, tun aranar farko da fareeda taga Abdul takamu da sonsa,, sai dai kash daga baya sai ya nuna k'awarta yakeso safiyya,, dan danan kuma soyayya mai k'arfi tashiga tsakanin Abdul da safiyya, wannan yasa fareeda ta danne son Abdul azuciyarta, sai dai kuma yau da gobe sirrin nata yana nema fitowa fili.
              """" dan duk ranar da fareeda taga Abdul yazo wajen safiyya takanji wani bak'in ciki da kishi,, har yakansa ta nuna fushinta afili,, duk da tasan k'awarta tata tana tsananin son Abdul,, wanda a yanzun haka ankai kud'in auren Abdul gidansu safiyya, harda saka rana,, za ayi bikinsu bayan ta kammala secondry.
         "Toko wannan aure zai yiwwu??ko fareeda zata hak'ura da k'udirinta kafin k'awar tata ta fargane??? kubiyoni dan tabba tarwa.........................✍🏻


💕Bily💕
💕💕Mrs Abdus'salam💕💕💕
💕I LOVE YOU MY FAN's💕💕
                                             💕
[12/19, 7:24 PM] mrs bilkisu: 3~October ~2016



🔷🔹NI    DA   K'AWATA🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💕 







🔶🔸3⃣🔸🔶


............yau takama weekend babu school su sopy suna gida, sopy ce zaune tana wanke wanken kwanuka inna na gefenta tana tsintar shinkafa 'yar hausa.
     "Safiyya! Wai bazakiyi sauri ki tashi awajennan ba ko?? Nafad'a mikifa yau kece zaki mana abinci, amma kin zauna wanke2 bawani mai yawaba sai lank'andi kikeyi, kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki.
Sopy ta turo baki gaba ALLAH inna ni bana son yin girkin nan mutum yayta fama da iccen nan, ga azabar hayak'i idonka yayta hawaye kamar kana kuka.
     Inna ta girgiza kai tana murmushi, nima d'in danake dafa miki kullum kizo kici haka nake fama, dan haka yau har girkin dare kezakiyi shi.
Sopy tazaro ido 😳kai inna da gsk kikeyi??
    Na tab'ayimiki k'aryane?? Inna tabad'a tana mik'ewa tsaye,, Sopy tace"A'a.
inna tace" to yimaza ki gama ki tashi rana tanayi kinsan babanki kuma yakusa dawowa.

Sopy tai shiru tana wanke2n ta can kuma saitace inna!!  Inna ta amsa da na'am.
Inna mizai hana ahad'e abincin harna dare?? A'a baza a had'eba kinsan dai babanku bason cin shinkarnan yakeba koda yaushe balle wannan fara da mai d'in, yana cine kawai dan bashida yanda zaiyi,, ayi shinkafar yanzu da daddare sai ayi tuwo.
     Tuwo kuma inna!!!! Jiyafa shi mukaci nikam nagaji da cin tuwonnan wlhy.
Inna ta d'auki wani murfin roba dake gefenta ta jefi safiyya dashi,, dan k'aniyarki in bakici tuwonba mizakici?? Ko kin ajiye mana wani abincinne bayan tuwon?? Kudai yaran yanzu bakusan ku godema ALLAH ba yayin dayay muku ni'ima, da basai ki wuni ki kwana bamuci abinci agidannan ba, amma yanzu ALLAH yarufa mana asiri shine zakiyima mutane iyayi,, kul nasake jin wannan furicin abakinki.
          "" Sopy tai kwal2 da idanu tana shirin yin kuka dan ganin ran innarta ya b'aci, tace" dan ALLAH inna kiyi hak'uri bazan sakeba ki gafarceni???
Inna tai murmushi to shikenan ya wuce share hawayenki kinji,, barma girkin nizanyi.
A'a inna kibari zanyi tafad'a tana nufar kichin d'in da hayakin wuta ya maida bangon bak'ik'k'irin, tafara k'ok'arin had'a wutar icce.
 
Sopy tana aiki suna hira da inna, inna tace waini lfy yau banga fareeda ba agidannan kuma kema banga kinje gidansuba????
     Sopy tace"wlhy babu komai inna, tacemin ne zataje gidan k'anuwar mama a hotoro, nikuma kinsan ba shiri muke da'itaba shiyyasa nace bazanjeba,, to inaga tana can bata dawoba.
   Hummm kudai kaiwai shirmenku ne ya motsa amma in banda haka miye nawani rashin shiri kema aii sadiya innar kice.
                  "Taf inna ALLAH yakiyaye sadiya tazama inna ta,, dan tunda nalura batasan abotarmu da fareeda nai alk'awarin na daina zuwa gidanta,, idan tazo nan anguwar ma gaisa, shima idan mun had'u kenan.
Inna ta shige d'aki tana fad'in kudai kuka sani.

::::::::::::::::::::::::::::::::::::☆
Fareeda tana gidan innarta sadiya, k'anwar mamace mahaifiyar fareeda, itamadai bawata babba bace dan kusan sa'ar hauwa'u ce yayar safiyya.
    Suna zaune afalon sadiyar gabansu tiren taliyane da yaji damai,, kunsan dai mu 'yan kano mun iya k'wad'ayin  mai da yaji, sadiya takalli fareeda 'yar uwa ina jinki jamuje labari.
 Fareeda ta harareta oh dama matsalar tawa labarice?? Sadiya tace yi hak'uri ina tsokanarkine.                                   """Fareeda taja ajiyar zuciya sannan takuma gyara zama tana fad'in wlhy anty da nayi niyyar bar mata Abdul amma yanzu bazan iyaba, idan nagansu tare jinake tamkar na had'iyi zuciya na mutu.
Dan ALLAH ki bani shawara miya kamata nayi????  Dan na mallaki Abdul.
           """Sadiya tayi murmushi aii wlhy koni ban goyi bayan ki bar mata shiba, Abdul k'yak'yk'awane dama dake yadace bawannan bak'ar yarin yarba,k'ilama asiri tai muku dan na lura tun farko ke yake so. Fareeda ta gir giza kai,, bana tunanin haka aunty sadiya nasan halin sopy nakuma san abinda zata iya,, inama tasan inda wasu malamai suke?? bare taje, kedai kawai bani shawara.

Sadiya ta tab'e baki dan ta lura fareeda bazata gane inda ta dosaba,, tace kawo kunnanki kiji!!!;!! 
Fareeda ta mik'a kunnenta ga sadiya, can kuma sai suka tuntsire da dariya harda tafawa, fareeda tace"wlhy shawararki tayi auntyna ALLAH ya biyaki,, inada tabbacin samun ABDUL yanzu. 
Tofa masu karatu wace irin shawar sadiya tabama fareeda ne??? dahar take murna haka, harma da tabbatar wa kanta samun ABDUL,, to kudai biyoni dan jin wannan bada k'ala.......... ..✍🏻



💕Bily💕
💕💕Mrs Abdus'salam💕💕💕
💕I LOVE YOU MY FAN's💕💕
                                            💕

4~October ~2016



🔷🔹NI   DA   K'AWATA 🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💕






🔶🔸4⃣🔸🔶

..............koda  yamma da fareeda tadawo bata  shiga gidan su Sopy ba, Sopy tagama shirin islamiyya ta fito,  inna bari nagani ko fareeda tadawo saimu wuce islamiyya idan kuma bata dawoba nisai na wuce.
     "" to autar inna adawo lfy""
Tafita tana fad'in ALLAH yasa innata.
 Da sallamarta tashiga gidan, mama dake zaune a k'ofar d'akinta tana linke kayan wanki, ta amsa da fara'arta,, Sopy ta tsugunna ta gaida mama.
  "Mama tace" waini yau ina kika shiga safiyya?? Duk yau ban gankiba, ince dai lfy???
Sopy tayi murmushi wlhy lafiya lao mama ina gidane kawai.
     Aii d'azu danaga fareeda ta shirya canake tare kuka tafi hotoron??
A'a mama batare mukajeba saboda zanyi wanki.
ALLAH sarki  kishiga tana nan tun d'azu tadawo inagama barci takeyi;

Sopy tamik'e tana fad'in fareeda kasace aii,, amma barcin yamma.
Tad'aga labilen d'akin fareeda kwance d'ai d'ai akatifa tana kwasar barci, Sopy tak'arasa cikin d'akin tasa hannu ta daki bayan fareeda, ke uwar barci tashi.
              "Fareeda ta taahi a firgice tana fad'in wayyo mama.......saitaga safiyya tsaye akanta,, Sopy tace sarkin tsoro kawai kin wani tashi afirgice kamar wadda aka firgita.
 Fareeda ta harareta wlhy sopy ke 'yar iskace miye na tashina ina barci??               
To badole natashekiba tunda ke bak'ya duba agogo, kullum kece kikeja mu makara a islamiyya.
Fareeda ta yatsine fuska aini inagama yau bazani islamiyyar nanaba.
     " saboda me??? Sopy ta tanbaya.
Babu komai kainane kawai keyimin ciwo.
Sopy tace" kinsha maganine?? A'a ban shaba amma yanzu zani nasiyo tunda kin tasheni,, tamik'e barima mufita tare.

Tare suka fito fareeda ta amshi kud'in magani awajen mama suka tafi,, dai2 zasu fita  kwanar layinsu suka gamu da ABDUL dawani abokinsa Adam,, adam yace" 'yan halak kunk'i ambato yanzu muke hirarku ashe kuna hanya.
      "CIkin zolaya Sopy tace" kodai kuna gulmarmu???
Abdul yace" kajiko abokina shiyyasa nace kayi shiru karka fad'a,, wad'an nan baka iya musu.
Adam yay dariya gsky ne abokina,, wannan abotar mai k'arfice nadad'e banga k'awaye masu irin shak'uwarkuba, gaku nan tamkar 'yan biyu.
       "" fareeda tace" lah bakada labarin mu 'yan biyune rana d'aya aka haifemu kaje ka tambaya.""
Adam ya jinjina kai aii bama saina tambayaba nayarda, dan abokina yatab'a fad'amin.
   "Abdul yamatsa kusada sopy gimbiyata yayadai?? 
Tai murmushi lfy lao habibina saidai my sister ce kanta yake ciwo.
Ayya ALLAH yak'ara sauk'i shiyyasa naga d'aya da uniform d'aya babu???
  Sopy tayi murmushi eh kusan hakane danni zanje islamiyya itakuma zata sayo magani ne.
          "Ayya sorry fareeda ALLAH yak'ara sauk'i."
 Amin fareeda tafad'a tana fari da idanu.

Abdul yakalli agogon hannunsa gimbiyata yakamata ki wuce dan zaki makara karkisha bulalar makarafa.
 Sopy tad'an murmusa gskyar ka habibina dan yasayyadi yananan abakin get, bari nawuce kasan idan ina tare dakai nakan manta kowa da komai.
            " nima haka gimbiyata Abdul yafad"a yana kashe mata ido d'aya,,, Adam yace" kuna sha aninku masoyan zamani,, itakam fareeda tayi kicin kichin da rai kamar zata fasa ihu,, sopy ta tab'ata sister barina wuce saina dawo ALLAH yak'ara sauk'i.
"Amin tafad'a ranta a dagule"
   Abdul yace" aii barima mu kaita k'yamis aduba miki ita.
Yawwa habibina nakwa gode maka,, bari nawuce sai da daddare mun had'u.
     "To shikenan ALLAH ya kaimu my lovely wife. 

Abdul yadawo da kallonsa kan fareeda bayan b'acewar sopy,, fareeda tad'anja k'aramin tsaki mara sauti,, Abdul yay saurin fad'in lfy?? Fareeda taid'an yak'e wlhy jinai kaina ya sara.
   Okey sorry to muje ko??
Adam yace" aii ni inaga anan zamu rabu, dan wlhy abba ya aikeni amma sai yanzu natuna, kuje da daddare zamu had'u insha ALLAH fareeda ALLAH yak'ara sauk'i,, saida daddare idan munzo tad'i.
To Adam nagode ALLAH yakaimu daren.
""Amin adam yafad'a,, sukai sallama yatafi suma suka tafi.

Tafiya suke cikin nutsuwa kowa da irin tunanin dayakeyi azuciyarsa, har suka isa k'yamis d'in sadiq amma k'yamis d'in arufe.
 Abdul yace" inaga saimunje k'amis d'in Rufa'i fa,, kozaki iya??
Tai murmushi babu damuwa muje nida nake neman lfy.
Shima murmushin yayi,, to shikenan muje.
              " sun isa k'yamis d'in Rufa'i aka bama fareeda magun guna,, Abdul yabiya suka fito,, saida sukaje bakin titi fareeda tace" Abdul idan bazaka damuba inason muyi wata magana.
   "Abdul ya kalleta to ina saurarenki,,fad'a min.
A'a maganar bata tsaye bace,, indai ban takuraka ba musami gurin zama.
Abdul yace" to inaga kibari saida daddare idan nazo saimu zauna muyi maganar mu uku harda Sopy, inaga hakan zaifi ko???
                   "Fareeda ta had'iye wani kududun bak'in ciki daya tsaya mata a mak'oshi,, jikake k'uuuuuttt!!!
Abdul yace hakan yayi ko?? Fareeda ta girgiza kai,, Alamar A'a,, tacigaba da fad'in mubiyu nakeson muyi maganar dan banaso Sopy tasani,, kasaka mana lokaci muhad'u nida kai kaiwai.
     Abdul yay shiru yana tunani, saikuma yaja numfashi, to amma miyasa baki son Sopy tasani?? Fareeda tayi d'an murmushi, babu komai wlhy amma bana son tasani saimun kammala komai sannan, inason nabata mamakine.
 Abdul yay dariya to shikenan babu damuwa,, saimu bari zuwa kamar weekend ko???
  Babu damuwa indai hakan yayi maka ni agareni babu matsala.
       "" to amma kina ganin tayaya zamu kasance tare dake batareda sopy tasaniba?? Kinsan koda yaushe kuna tare.
  Indai wannan ne babu matsala nasan yanda zan kauce mata.
 To shikenan Abdul yafad'a yana kallon fareeda,, har gida yarakota sannan yajuya,, amma zuciyarsa tana tunanin mi fareeda keson fad'a masa wanda batason safiyya tasani ??? Hakadai yayta tunani har yak'arasa majalissarsu inda suke zama da abokansa da yamma bayan kowa yadawo aiki ko kasuwa.
To masu karatu kubiyo  danjin  mi fareeda zata fad'awa Abdul ne??? Shin idan ta fad'a masa zaya amince????? Kubiyo ni danjin amsar tan bayoyinku. .................✍🏻



💕Bily💕
💕💕Mrs Abdus'salam💕💕💕
💕I LOVE YOU  MY FAN's💕💕
                                              💕
5~October ~2016



🔷🔹NI   DA  K'AWATA 🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM 💕




🔶🔸5⃣🔸🔶


...................fareeda tafito cikin sharin fita, mama tabita da kallo kekuma ina zakije da yamman nan???
Mama dan ALLAH kibarni naje gidan aunty sadiya gobe in ALLAH yakaimu da safe saina dawo tunda babu makaranta.
      Mama ta harareta kinga fareeda kifita idanuna tunkafin na b'ata miki rai,, yaufa kwananki uku da zuwa gidan sadiyar shine yaukuma kice zaki koma,, to waima mizakije yine??
      : : fareeda ta turo baki gaba nifa sak'o zan amso awajenta.
Sak'o kuma??? To sak'on mi?? Kuma waye yabada sak'o abaki??
Fareeda tayi shiru dan batasan abinda zata fad'awa mama tabarta zuwaba,, saikawai tacire gyalen ta ajiye saman igiyar shanya,, tana fad'in tunda dai kin hana shikenan.
Mama tai tsaki ke dai kika sani.

Sopy kwance atsakar gida jikin wata 'yar bishiyar mangwaro dake tsakar gidansu,, hannunta rik'e da littafin English tana dubawa, dan exam tana gabatosu,, inna dake zirga zirga a tsakar gida dan k"ok'arin had'a abincin dare, ta kalli sopy safiyya ki tashi ki share tsakar gidannan kar magriba tayifa kina ganin rana tafara jaa.
  To inna safiyya tafad'a tana mik'ewa, ta nannad'e tabarmar tafara sharar tsakar gidan,, tana cikin sharar malam ibrahim yay sallama da gudu sopy taje ta taryoshi,, baba sannu dazuwa.
 Yauwa safiyan baba,, ya gidan?? Wlhy baba kafiya lao, to madalla.
Ta karb'i ledan hannunsa tana fad'in baba mika sayomin???
 Yay dariya safiya way sai yaushe zakibar kwad'ayine kinfa girma,, inna tafito kichin tana masa sannu ya amsa cikin fara'a,, yaja kujera 'yar tsugunno yazauna,, inna takawo masa ruwansha.
Sopy tagama shara ta wanke hannunta, sannan tanufo babanta, baba tunda kaki fad'a min nibari naduba dakaina,, baba yay dariya to duba 'yar baba kankanace nasiyo miki saboda nasanki da son kankana,, ta d'auki ledar tana fad'in nagode babana mai sona.
Inna tace" malam ita kad'ai kasayoma kankarar Kenan? ?? Safiyya tace kai inna kina kishine???
Inna taimata 🖐🏻dak'uwa kinci gidanku nicema nake kishin dake ???
Malam ya mik'e yana musu dariya,, yad'au buta yayi alwala, ita kuma Sopy tazauna gyara kankana, dan tana fashin sallah.

Suna zaune atsakar gida suna cin abinci,, sopy tana gefe tana shan kankana,, inna tace" ni ina tawa kankanar?? Sopy tamik'e tana fad'in wlhy baba idan banbama inna kankanar nanba bazata barni nasha iskaba.
            " inna tarik'e baki wayni yaushe safiyya ta rainani agidannan ne malam??? Malam ibrahim ya murmusa bawani raini,, aii ko kurama da 'ya'yanta take wasa a dawa,, itama tana tsokanarkine kaway.
Inna tace" kaidai kana goya mata baya ne kaway,, safiyya tai dariya baba kabarta ai kwanannan zan tafiyata gidan aunty Nafisa hutu saita dad'e bata ganniba,, damma uncle kabeer bashida mata da gidansa zan koma.........yaron dayay sallama yasa sopy yin shiru.
        "" kai shamsu lfy ??sopy ta tanbaya,, shamsu yace wanine yace kizo awaje,, wani kuma?? Waye wani?? bashida suna ne??? Shamsu yace nibansan sunansaba amma agidan Alhaji Abubakar mai fata yake.
  Baba yace"kaga yaro yitafiyar ka,, gata nan zuwa. 
Sopy ta turo baki wlhy nikam baba banason fita tad'innan yau,, baba yace"" tobake kika zab'i mijinkiba da kanki maza tashi kije,, amma kar a zauna wannan doguwar hirar,, tun ana fad'ar gsky har akoma k'arya.
   Sopy tace"to baba bari nak'are shan kankanata.
A'a tashikije idan kin dawo saikisha.
Dole tamik'e tatafi badan tasoba.

Inna ta kalli baba,, malam wlhy nidai dan kawai safiyya tanason yaron nan amma nikam bai kwanta min araiba,, banaso akai safiyya gidan nan mai tarin mata da 'ya'ya.
Baba yaja ajiyar zuciya,, hajara babu abinda zamu iyayi face addu'a,, dan neman zab'in ALLAH, ALLAH yazab'a mana abinda yafi alkairi.
               "To amin malam"

Awaje kuwa sopy tana fita  saita tararda  Abdul tare da fareeda suna hira,, lamarin yayi matuk'ar bawa sopy mamaki,, amma saita danne tak'arada wajensu da sallama.
   Atare suka amsa mata,, takalli fareeda,, ke sister amma ke 'yar rainin hankalice yanzu nan dama baki tafiba???? Fareeda tace" kibari kawai 'yar uwa wlhy mamace ta kwafsa min tahanani zuwa,, fushi nakeyi shiyyasa kikaga ban shigoba,, yanzuma nazo na ari wayan Abdul ne nakira aunty sadiya nafad'a mata abinda yahanani zuwa.
                 
                Sopy taja ajiyar zuciya mai k'arfi,, Abdul yay saurin kallonta gimbiyata miye matsalarki????  Babu komai habibina ykk?? Lfy lau nake gimbiyata.
  Nan dai suka dasa hira harda fareeda,, dan tak'i tafiya.
Hakan baisa sopy ta zargi komai ba, dan zuciyarta a tsarkake take,, ta yarda da fareeda da Abdul, d'ari bisa d'ari.

 Washe gari saiga aunty sadiya tazo gidansu fareeda,, nanta wuni,, saida mama tashiga sallah sannan aunty sadiya tabama fareeda abinda takawo mata,, tai mata bayani dalla dalla sai dai nima bansan mita bataba masu karatu dan sunshige k'uryar d'akine.
           " kukasance tare dani danjin yanda zata kasance.....................✍🏻



💕Bily💕
💕💕Mrs Abdus'salam💕💕💕
💕I LOVE YOU MY FAN's💕💕
                                            💕

[12/19, 7:24 PM] mrs bilkisu: 6~October ~2016



🔷🔹NI   DA  K'AWATA🔹🔷


NA BILKISA IBRAHIM💕




🔶🔸6⃣🔸🔶


................Yaud'in takasance asabar babu makaranta su sopy suna gida,, fareeda ce tadoso gidansu sopy hannunta rik'e da filet a rufe tashigo da sallama,, inna dake d'aki ta amsa mata,, tak'arasa d'akin inna ta gaisheta inna tace" yasu ladidin?? Lfy lao inna tamace na gaisheki wai anjima zata shigo kuje asibitin dubiyar nan.
    "" A toshikenan babu damuwa saita zod'in,, kishiga safiyyan tana nan a d'akinta tana shirin tfy gidan hauwa'u,, nazatama tare zaku??? Eh dama tare zamuje to sai zanje gidan aunty sadiya nakai mata sak'o kinsan ita kuma bata zuwa gidan,, amma inna kai sak'on zan isketa acan d'in.
Ato shikenan ma,, itama d'in shirmene yake damunta kawai,, sadiya ba innarta bace??
   Fareeda tayi murmushi bahaka bane inna laifin aunty sadiyarne aii,, tafad'a tana mik'ewa.

D'akin sopy ta shiga, sopy na zaune tana kwalliya fareeda ta zauna kusada ita 'yammata wannan irin kwalliya haka' saikace maishirin zuwa gasa???         Sopy ta harareta ke bakiga takibane??? Nitunda nake dake ma bantab'a ganin kinyi irin wannan gayunba wlhy????
         "Fareeda ta tura mata filet d'in datazo dashi, tana fad'in shike nan kin rama.
Sopy ta bud'e filet d'in tana fad'in mikika kawo min??
Wlhy waynar filawace nayi dasafe,, to naga baki shigoba shiyyasa nabiyoki da ita.
       Sopy tace" kin k'yauta kuwa dama tund'azu nakasa karyawa.
     " saboda mi??
Wlhy bako mai kawai dai yaunatashi duk jikina babu dad'i ga gabana sai fad'uwa yakeyi.   Fareeda tace tofa lfy dai""
 Wlhy nima bansaniba 'yar uwa.
To ALLAH yatabbatar mana da alkairinsa,,, fareeda tafad'a.
  "" sopy tace'' amin dai.

Tare suka fito kowacce tahau mota zuwa inda zata.
 hauwa'u tatari 'yar uwarta da murana,, sopy tace" aunty ina Arfat yake?? Yana wajen kareema yarinyar makwaftan mu d'azunnan tazo ta d'aukeshi suka tafi.
  " kai aunty wanan d'an yaron kika bari aka fita dashi da wannan safiyar?? To yazanyi auta yariga yasaba dasu,, tashigo kawo min abune yamak'ale mata. Toni dai ki aika akawo min yarona! Karki damu  zata kawoshi,, wai yana ganki ke kad'ai ina K'AWAR taki fareeda???
   "Itama tana nan zuwa taje gidan sadiyane takai sak'o zuwa anjima zata zo.
To shikenan ALLAH yakawo ta nitashima ki d'ora mana abincin rana,, dama d'inki zanyi.
  Kefa kinji matsalarki mutum baya zuwa gidanki ya huta dayazo saikin manna masa aiki, tafad'a tana kumbura baki.
 Aunty hauwa'u tace" kekuma gashi baki son aiki ko?? Haka zamu kaiwa Abdul d'in ke,, inma zaki dage kidage wannan gidan nasu mai tarin 'ya'ya da mata,, dan agidan za'a ajiyeki tunda dukkan matan yayyensa anan suke zaune.
Sopy ta tashi daga kwanciyar datayi,, to aishi yace" ba anan zamu zaunaba zai kama mana haya.
 Aunty hauwa'u ta tab'e baki to ALLAH yasa hakane???
       "Sopy tamik'e tana fad'in hakanema.
Miza'a dafa?? Aii inaga tuwon shinkafa za'ayi. Sopy tace" kai kukam kuda inna bakuda matsalar data wuce ta tuwo?? Aunty hauwa'u tai dariya,, toshi abban Arfat yakeson ci.
  Nikam gsky bazanci tuwo daranaba,, zan dafa mana wani abu nida fareeda kafin tazo!   Duk yanda kikayi cewar aunty hauwa'u.

Fareeda kam ta isa gidan aunty sadiya,, sadiya tabita da kallo lallai fareeda wannan irin kwalliya haka??? Duk ta tarar Abdul d'ince??? Fareeda tayi dariya auty sadiya ya rankine,?? kefa kikace na cake sosai.
       " sadiya tace" gsk yane d'iyata, suka tafa nuna dariya.
Fareeda tace" yaya dai kin kammala girkin??
 Aii komai ya kammala yanzu Abdul kawai zamu jira.
Fareeda tai wani ihu ALLAH yabar minke aunty na,, kina cikin aikina.
Sadiya tai dariya ALLAH yashir yaki fareeda,, yanzu dai ki kirashi dan muji yaushe zai iso??
"" to auntyna, fareeda takira Abdul yacemata aii gama shinan ahanyar zuwa,, tak'ara yimasa kwatancen layin?? Fareeda takuma yimasa kwatance sannan ta kashe wayar.

Sopy tagama abinci tazauna kusada aunty hauwa'u tana fad'in wash ALLAH yaudai saina sha maganin gajiya zan iya barci.
Aunty ta harareta way safiyya mikike son zamane?? Da dai keba raguwa bace wlhy.
Sopy tai dariya dama can dan ban gama sanin ciwon kaina baneba,, amma yanzu ina.
      "" aunty tace" zaki gaya musu yarinya.
Kareema tai sallama hannunta d'auke da Arfat,, sopy ta karb'eshi da sauri tana fad'in oyoyo my son! Tai kissing d'in kumatunsa.
     "" kareema ta gaisheta,, aunty hauwa'u tace kareema sannun ki! Kareema tai dariya kai aunty saikace wani aiki,, umma cema tace nakawoshi yasha nono amma ba kuka yakeba. 
  Aunty hauwa'u tace" aii nagode wlhy badankeba da Arfat bazai barni nayi d'inkin nanba,,, nibansan yanda zanyiba idan kinyi aure??? Kareema tafita da gudu wai kunya takeji,, su sopy sukasaka dariya.......................✍🏻



💕Bily💕
💕💕Mrs Abdus'salam💕💕💕
💕I LOVE YOU MY FAN's💕💕
                                            💕
[12/19, 7:24 PM] mrs bilkisu: 7~October ~2016


🔷🔹NI   DA   K'AWATA 🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💕



🔶🔸7⃣🔸🔶


..............Abdul ya iso yakira fareeda yay mata kwatancen inda yake,, suka aika wani yaro ya taho dashi zuwa k'ofar gidan,, amma sai yaja tunga yak'i shiga gidan,, fareeda tafito cikin dogon hijjab harda saka nik'af shi baima ganetaba dan haka yad'an ja gefe domin bata hanya,, tai masa sallama ya amsa yana binta da kallo,, tai dariya Abdul nicefa fareeda baka ganeniba ne??
 Abdul yace"tofa wlhy ban ganekiba naga kinsaka nik'af nina zatama matar aurece!! 
Fareeda tai dariya wlhy nice,, kashigo mana!!
    A'a yaza ayi nashiga gidan mutane batareda izinin mai gidan ba???
 Karka damu baya nan kuma yasan da zuwanka, kashigo kaway dan ALLAH.
sayda yay jim sannan yace" kina ganin babu matsala fareeda!
Babu wata matsala kamar yanda nagaya maka yasan da zuwanka,, kafinma katafi zai dawo gidan.
     " to shike nan muje"
Har falon aunty sadiya suka kaishi yazauna yana shak'ar iskar fanka,, fareeda tafito zuwa tsakar gida ta iske aunty sadiya a kichin,, aunty sadiya tace" yaya dai yashigo?? Fareeda tace" yanama falonki zaune. Sukai dariya, sopy tacire nik'abi tad'au wata hoda a cikin leda ta kuma shafawa ta d' au kwalli tashafa,, aunty sadiya tamik'o mata turare ta fesa,, sannan tace" nayi my aunty??? Sadiya ta jinjina kai kinyi d'iyata komai yaji,, d'auki abinci kitafi nima zanzo mugaisa.
 To shikenan auntyna fareeda tafad'a tana d'aukar tiren da kulolo ke kai.

Tai sallama ak'ofar palon cikin irin wata murya wadda itama batasan tana da itaba,, Abdul ya amsa tareda mik'ewa yatarota tiren hannunta ya karb'a yana fad'in wannan tire haka aii yayi miki nauyi dayawa.
 Fareeda tazauna tana murmushi Abdul yad'ago suka had'a ido,, jiyay wani abu yashige jikinsa tundaga kansa har zuwa yatsun k'afarsa,, yarintse ido yana fad'in yasalam!!
Fareeda tace"Abdul yaya dai???
Yasakar mata tsadadden murmushi babu komai ina cikin wani irin farin cikine dana kasance dake.
    "Fareeda tace" tofa Abdul nikuma?? Ko ka manta ba gimbiyarka bace sopy??
Abdul ya b'ata rai kinga idan muna magarmu ki daina sako mana wata sopy.
Fareeda tayi murmushi to nabari my love kayi hak'uri kabar b'ata ranka.
        ""Fareeda tazuba lemo akofi tabasa, yakarb'a yashanye,, takalleshi abincifa,, yay mata murmushi abani naci dama kamshinsa yanata cikamin hanci.
Fareeda tazuba masa farar shinkafa da miya yaci ya k'oshi suna hira,, saida yagama suka nutsu,, fareeda tace" Abdul yamaganar mune??? Abdul yay mata wani kallo na masoyi zuwa masoyiyarsa yace"ina saurarenki aii dama maganarce takawoni gareki my love!!
 Fareeda tai wani murmushin mugunta tace" yayi k'yau,, tasowa tayi tadawo kujerar kusa dashi, takanne masa ido d'aya yay murmushi.
Shima yajuwyo sosai suna kallon juna,, suka k'urama juna ido kamar zasu cinye juna,, fareeda ce tafara janye nata idon tana murmushi,, cikin karsashi tace"my Abdul!!!!
Abdul ya amsa murya asark'e.  Taja ajiyar zuciya Abdul ina matuk'ar k'aunarka fiye da mai buk'atar ruwa acikin sahara,, ina begenka fiyeda d'an da ke buk'atar nonon mahaifiyarsa alokacin dayake kuka, ina son kasancewa dakai tamkar bawan dake k'aunar bud'ar ido yagansa a aljanna, ina burin tara zuri'a dakai fiyeda talakan da ke burin tara dukiya, ina burin kozamu mutu mu mutu tare tamkar laila da majnun.
Hawaye suka zubo akuma tunta, Abdul yasa hannu yashare mata hawayen,, cikin sark'ewar murya yace" nima ina sonki fareeda ina k'aunarki, ina burin aurenki, ki kwantar da hankalinki insha ALLAH kece uwar 'ya'yana.
   Fareeda tad'ago kai dasauri tana kallonsa dan ALLAH Abdul da gsk kake???
Abdul yay murmushi da gsk nakeyi fareeda insha ALLAHU zaki zama matata.
  " fareeda tai dariyar farin ciki,, tace" to amma yanzu yaza muyi da sopy???
Abdul yace" zan fad'a mata bana ra'ayinta yanzu, kece ra'ayina!!
A'a Abdul bahaka za'ayiba kawo kunnanka kaji!! Abdul yamik'awa fareeda kunnansa tafad'a masa,, yay wani murmushi yace" (nice idear) hakanma yayi,, nandai sukaita hira suna zazzagema juna sirrin zuciyarsu.

Agidan aunty hauwa'u kuwa sopy nacan tana jiran fareeda kad'an kad'an saitayi tsak'i, aunty hauwa'u tace auta way miye matsalarki ne???
Sopy tai d'an tsaki wlhy aunty haka kawai yau sai gabana ke fad'uwa tunda safe,, ga fareeda daga kai sak'o amma shiru kakeji kamar an aiki bawa garinsu.
 Aunty hauwa'u tace" k'ila gosulo ne yarik'e ta,, zatazo tunda tace miki zatazo,, fad'uwar gaba kuma kita addu'a insha ALLAHU babu abinda zai faru sai alkairi.
 Sopy tace" to ALLAH ya tabbatar mana da alkairin.
Kubiyoni masu karatu,  danjin yanda zata kasance..................✍🏻




💕Bily💕
💕💕Mrs Abdus'salam💕💕💕
💕I LOVE YOU MY FAN's💕💕
                                            💕
[12/19, 7:24 PM] mrs bilkisu: 8~October ~2016


🔷🔹NI   DA  K'AWATA 🔹🔷


NA BILKISA IBRAHIM💕



🔶🔸8⃣🔸🔶


................Sai wajan k'arfe 3:30 suka baro gidan aunty sadiya, Abdul ya kalli fareeda my love!! Yanzu "k" ina kika nufa??
Tai fari da idanu zanje wajen gimbiyarka ne a d'orayi, dan tana gidan aunty hauwa'u tana jirana.
Yad'an gintse fuska wato wannan gimbiyar bazai fita a bakinkiba ko??
Tai murmushi kayi hak'uri,, amma naga kaine kasaka mata gimbiyar aii?? Eh nine nasaka mata amma a da ba yanzuba,, yanzu kece gimbiyata! Dan haka karna sake jin wannan sunan wlhy natsaneshi.
 Ta murmusa insha ALLAH wannan sunan ya goge har abada kamar yanda ALLAH ya shafe FIR'AUNA DA ABU LAHAB a doron k'asa.
       "" Abdul yay murmushi harna k'ara sonki my love!!
Itama tai dariya to ALLAH yak'ara maka sona my love!! Amin Abdul yafad'a yana kallonta,, yacigaba toni bari nawuce gida dansu adam nacan suna jirana zamuje fagge.
Okey to saikun dawo,, nima bari nak'arasa dan nasan sopy nacan hankalinta atashe tana zura ido taga ta inda zan b'ullo.
    Abdul yace" okey yazaro dubu d'aya yabata ga wannan kiyi k'ud'in mota,, tace to nagode,, saida yaga tashiga mota sannan yatafi shima.

Fareeda tanufi d'orayi cikin farinciki,, irin wanda daka ganta zaka shaida haka.
Ta isa gidan aunty hauwa'u sopy ta harareta aii dama kin koma saimu had'u agida.
Fareeda ta rungume sopy tana fad'in sorry my dear sister wlhy matsalar gosuloce kuma na tarar aunty sadiya bata nan nad'an dad'e kafin tadawo,, plz for giveme my sweet sister ayi hak'uri Amin azuri,, auntyna kisa baki a yafe min.
Aunty hauwa'u tayi dariya karki damu zaku daidaita nasani aii babu mai shiga tsakanin masoya.
     " sopy ta tuntsire da dariya ALLAH dandai kawai na yarda dake,, amma da watace sainayi sati bamuyi magana ba.
  Fareeda tace" to nagode my darling da kika yarda dani.
 Sopy tace" to zauna nakawo miki abinci.
Nan sukaita hira abinsu,, sopy tace" way my sister miye yasaki farin cikine?? Naganki yau cikin irin wata walwala ta musamman; fareeda tayi dariya kibari kawai 'yar uwa wlhy ina cikin farin ciki mai tarin yawa.          Tofa k'awata miye sirrin???
     "Fareeda tayi dariya nima ban saniba amma ki tayani da addu'a.
Sopy ta dafata to ALLAH ya tabbatar mana da alkairi my dear sister, nikuma kinga yau sai gabana keta yawan fad'uwa bansan daliliba??
 Kema aikairine my sopy.
Nan dai sukaita hirarsu har saida mijin aunty hauwa'u yadawo yana tsokanarsu,, my jidda yaukuma mafarkinmu tagwayen inna sukayine?? Aunty hauwa'u tayi dariya kamar dai hakane abban Arfat nima nayi mamakin ganinsu, dan yauma girkinsu aka kaimaka kasuwa.
 Haba shiyyasa naji girkin bai dad'iba yafad'a cikin tsokana.
      "" sopy tace haba na robar kaidai fad'i gsky nasan yau kaci girki ba irin namatar kaba, zauna kabamu labarin santin dakayi akasuwa.
Gaba d'aya suka kwashe da dariya hauwa'u tace" autafa ya isheku kubarmin miji yasha iskar duniya,, abban Arfat yace" barni dasu my jidda aii duk zan iya dasu ba baki suka fini ba.

Haka sukaita hirarsu da wasa da dariya sai gab da magriba suka tafi gida.
  "" kubiyoni masoyana,, ina k'yaunarku kamar yanda kuke son kasancewa dani a books d'ina, ina muku fatan alkairi akoda yaushe...................✍🏻



💕Bily💕
💕💕Mrs Abdus'salam💕💕💕
💕I LOVE YOU MY FAN's💕💕
                                            💕
[12/19, 7:24 PM] mrs bilkisu: 9~October ~2016


🔷🔹NI   DA  K'AWATA 🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM 💕



🔶🔸9⃣🔸🔶


...............Yau tsawon kwana hud'u kenan Sopy bataga Abdul ba, duk ta damu dan tunda suka had'u baitab'a kwana biyu baije gidansuba,, amma yanzu har tsawon kwana uku baizoba, gashi tana jin kunyar zuwa layinsu duboshi tagayawa fareeda tun jiya amma tace mata inkaji shiru to lfy ce,, itakam bata gamsu da wannan dalilinba,, wannan ne karo na farko dataji haushin rashin kasancewar waya a hannunta,, datanada waya saita kirashi kodan taji lfy?? Toko wayar baban ta zata amsa to saidai kuma batada nomber Abdul d'in tad'anja tsaki mara sauti,, kai bari uncle kabeer yazo zance masa ya saya min waya kodan irin wannan ranar,, ALLAH dai yasa ya amince kar yace saina gama makaranta.
Fareeda ta tab'ata,, tai firgigit alamar dawowa daga tunani,, sopy way mi kike tunanine inata magana tun d'azu amma kinyi shiriru miye matsalarki ne???
Sopy taja ajiyar zuciya matsalata dai d'ayace kamar yanda kika sani fareeda,, wace matsala kenan?? Fareeda ta tanbaya??  Sopy tace" matsalar Abdul mana,, yaufa tsawon kwana hud'u kenan baizo wajena ba!!
Fareeda tad'an tab'e baki,, aii nafad'a miki lfy itace ke b'uya amma ba ciwoba,, toki kwantar da hankalinki  yanzu haka daga gidansu Abdul nake..
Da sauri sopy tace" dan ALLAH da gsk kikeyi?? Fareeda ta b'ata rai tunda mike dake natab'a miki k'aryane??? Sopy tace"A'a" tokuma fareeda ta fad'a, dama bawani abune ya hanashi zuwaba wani aikine abbansu yasakasu,, yace" nabaki hak'uri shima yayi missing d'inki amma zuwa gobe zaizo.
      "" sopy ta sauke ajiyar zuciya kai wlhy harnaji dad'i, amma wlhy habibi yad'auki hakkina basai yasanar minba.
Fareeda tace" kedai ki masa uzuri tunda bai tab'a aikata miki maka mancin hakaba.
Sopy tace" hakane kuma na fahimce sa,, kema ngd miki abin k'aunata aminiyata mai sona da son farin cikina,, yau zanyi barci mai dad'i kenan tunda naji dalilin rashin zuwan rabin raina gareni.
  Fareeda ta harareta amma bata ganiba, azuciyarta tace" ko ubanki neshi dole ki barshi.
Amma afili saitace lallai kam yau sai ayi barci harda munshari tunda anji labarin habibi.
           " Sopy ta kai mata duka fareeda ta kauce tana dariya, itama sopyn dariya take, tace sister dan baki san so bane amma kibari inkin fara zaki san zafinsa dakuma dad'insa.
Fareeda ta tab'e baki tana fad'in naga lailah da majnun indai asoyayyane.
Nan dai sukata hirarsu.

Shikam Abdul kullum saiyazo wajan fareeda hira amma abayan layinsu suke hirar a soron gidan k'anin babanta'' wannan yasa sopy bata tab'a ganinsuba, ko wani d'an anguwar bare akawo mata gulma.
 Bayan tafiyar fareeda ma saita nufi inda suke had'uwa da Abdul, dan tasan yana can yana jiranta,, aiko kamar yanda tai tunani yana can zaune yana jiranta,,Tashiga soron da sallama, tazauna kusada Abdul ayya my love! Kayi hak'uri dan ALLAH nabarka kai kad'ai,, Abdul yay mata hararar wasa dama k'yace haka tunda kin barni ni kad'ai tun d'azu nake zaune anan yafad'a yana kallon agogon hannunsa.
     "" kayi hak'uri dan ALLAH ina wajen mutuniyar ka, dan ta tada hankalinta saboda rashin ganinka,, ya yatsine fuska wacece kuma mutuniyata?? Fareeda tayi dariya kana da wata mutuni bayan sopy?? Ya harareta mutuniyar ki dai dan dama tare naganku, gashi kuma nabarku tare,, dan hakama kibar had'ani da ita.
 Fareeda tad'an zaro ido waje tofa har lamarin yakai haka?? Abdul yace" aii yama wuce haka,, kinga nibama wannan ne agabanaba,, akwai abinda yakawoni.
         "" fareeda tagyara zama to miye ketafe dakai my love!! Ya shafa sumar kansa fareeda akwai matsalafa! Matsala kuma wace irin matsala!!!  Fareeda babana yak'i yarda da batun aurenmu dan yace bazai zama k'aramin murum ba,, bayan ankai kud'in aurena da safiyya yanzu kuma nace wata nakeso ba itaba,, wlhy nayi iya bakin k'ok'arina danya fahimta amma ina yamak'i saurarena.
  Fareeda tai shiru tana tunani, zuwa can taja ajiyar zuciya, takuma gyara zama my love! to idan abba yak'i ita kuma ummafa??
Yaja ajiyar zuciya ita umma dama batada matsala, dan duk abinda nakeso itama tana  sonshi kinsan ni d'an gatantane,, kodana fad'a mata catayi ALLAH ya zab'a mana abinda yafi alkairi.
 Fareeda ta lankwasa yatsun hannunta sukai k'ara tace" karka damu my love! Shima abban zai yarda da buk'atarka.
 Abdul yace" ta halin k'ak'a zai yarda abbana yanada taurin kai fareeda. 
Fareeda tai murmushi karka damu kabar komai ahannuna wannan aikinane.
Yace" to shikenan,, fareeda  tace" saidai matsala d'aya ke damuna,, yay saurin cewa wace matsala kuma?? Tace" matsalar sopy mana, tana cikin damuwar rashin ganinka yanzu haka saida nai mata k'arya sannan ta kwantar da hankalinta.
   Banason dukkan al'amarin aurena yashafi gidansu sopy bare harta zargi wani abu, nafi son kozata san hakan to yazamto an d'aura aurenmu,, alokacin kome zai faru yafaru tunda an d'aura nasan daga baya kowa zai hak'ura yabarmu.            Abdul yace" ke nifa ayanda nake jina bana tsoron kowa yasan sirrin zuciyata harda safiyya kuma aciki.
 Fareeda ta girgiza kai A'a my love!! Nikam bana fatan faruwar hakan,, har yanzu zuciyata da ruhina suna k'aunar safiyya, bakuma nason abinda zai cutar da k'awancen mu,, kuma bana son ka k'ub'cemin yanzu,, dolene mu dai daita tafiyar mu domin kawcema b'acinran sopy.
Yace" to ta yaya?? Tace" kawo kunnanka kaji,, yamik'a mata kunne ta fad'a masa,, yad'aga kafad'a tareda tab'e baki idan kina ganin hakan zai kwantar miki da hankali sai nayi.
 Tace" eh my love! Hakan zai sakani farin ciki,, ya murmisa to babu damuwa nibari na wuce sai da daddaren zaki ganni nazo.
To shikenan suka mik'e tare yanufi gida ita kuma tashiga gidan k'anin babanta domin gaishesu.

KIRA:- kai jama'a cin amana bashida k'yau yanzu idan kaine ko kece haka ta kasance dake kamar yanda take shirin kasan cewa da safiyya dan ALLAH yazakiji?? babu cin amana mai ciwo kamar irin ta wanda kafi k'auna ko ka amince dashi ka yarda dashi,, irin wannan cin amanar yafi zafi da ciwo,, yafi karya zuciya da bak'in ciki,, amana abune mai girma dan tana d'aya daga cikin alamomin MUNAFIKI, akwai irinsu fareeda da dama acikin al'umma,, samari da 'yammata, k'awa da k'awa, aboki da aboki,, masu aikata cin amana,, wad'anda suka maida cin amana bakomaiba acikin laififfikan duniya,, to "UBANGIJI ALLAH" ya shirya zukatanmu ka ganar damu gsky. Amin ya "RABBI"

Ku biyoni danjin yanda zata kasance....................✍🏻



💕Bily💕
💕💕Mrs Abdus'salam💕💕💕
💕I LOVE YOU MY FAN's💕💕
                                            💕
[12/19, 7:24 PM] mrs bilkisu: 10~October ~2016



🔷🔹NI   DA  K'AWATA🔹🔷


NA  BILKISA IBRAHIM💕



🔶🔸🔟🔸🔶


...............Da daddare Abdul ya aiko kiran sopy,, cikin zumud'i tasaka hijjab tafita,, inna ta girgiza kai tana fad'in yaran zamani basu san kunyaba dai.
 Inda suka saba zama ta iskeshi zaune, saidai fuskarsa babu walwala tak'arasa gareshi,, Assalamu alaika ya habibina,, yad'an kalleta batare daya amsaba, ya maida kansa kan waya.
        " tazauna inda tasaba zama sai kuma jikinta yafara sanyi,, tace" habibina ina yini ?? Ykk? Ya kwana biyu?? Wlhy nayi missing d'inka."
Yad'ago yana kallonta "k" irin wannan surutu haka bakinki baya gajiya?? Cikin mamaki sopy take kallonsa danjin furicin bakinsa,, ta daure tace" habibina miye matsalarka??
Yad'an yatsine fuska yana bin jikinsa da kallo,, sai kuma yakalleta "k" anaki tunanin minene matsalar ABDALLAHI ?? tad'anja numfashi habibina inda nasani aii bazan tanbayekaba sai kawai na fara maganinta.
        "" yace to banida wata matsala nikam.........kafin yarufe baki fareeda ta k'araso tana tafa hannaye,, suduka suka maida kallonsu gareta, dan danan fuskar Abdul ta sauya zuwa farinciki,, yace" sannu da zuwa m....... saikuma yayi shiru daya tuna gaban wadda yake, fareeda tak'araso tazauna kusada sopy tana fad'in yaudai sai abarmu muhuta ga habibi yazo.
    Sopy tad'an rankwashi kanta ALLAH fareeda kinga gurin barcina,, Abdul ya tuntsure da dariya wadda shima kansa baisan tamiye ba,, suduka suka bishi da kallo,, sopy tace" my sister kinga habibi ko tunda yazofa yak'i wani sakin jiki dani tamkar surukarsa ko mak'iyyarsa,, saifa da kikazo yay dariya.
    " fareeda ta tuntsure da dariya,, aidama tunda nazo dole film d'in ya k'are,, inba hakaba yasan zan tona,, dama yace" idan yazo gunki zai canja miki dan yaga ko kin damu dashi?? Sopy tad'an harari Abdul kai habibina ALLAH kad'auki hakkina,, yay murmushi wanda saida fareeda ta k'yafta masa ido yayishi,, yace" tokiyi hak'uri bazan sakeba kinji,, nan dai suka cigaba da hira,, mafi yawan hirar fareeda ce ke control d'in Abdul idan zai kauce hanya,, dan idan sopy tayi magana saikaga yaji haushi sai fareedan tayi saurin gyara masa,, da hakadai akai firar kowa ya kama gabansa,, badan hirar tayima sopy dad'iba.

Haka rayuwa taci gaba da gudu da sauri,, su sopy suna zuwa makaranta,, kuma k'awancen su natafiya kamar da yanda yake,, sai dai fareeda tana cin dunduniyar sopy batareda sopyn ta fargaba,, domin tayarda da fareeda d'ari bisa d'ari.
Abdul kuwa yanzu ba kullum yake zuwa gidansu ba, saima ya had'a kwana hud'u biyar bai zoba,, sai idan fareeda ta matsa masa da magiya sannan yazo,, wannan lamarin ne yasaka sopy cikin matuk'ar damuwa, ga exam  tana gabatosu, ga damuwa ta hanata maida hankali akan karatun,, duk k'arshen sati uncle kabeer saiyazo yayi musu bitar karatu amma ya lura kwata kwata sopy bata fahimta,, ya tsareta da tambayoyi tace masa babu abinda ke damunta,, daya kula bazata sanar dashi damuwartaba sai kawai yakoma lallashinta damata nasiha.

Ahankali inna tafara fahimtar matsalar sopy,, inna takira sopy ta tsareta saita fad'a mata abinda ke damunta,, harta rame haka sai tsawo kamar daren sallah,, sopy bata b'oyema inna komaiba ta fad'i damuwarta,, inna ta rarrasheta da alk'awarin tayata da addu'a.
          "Ana cikin haka suka fara (S,S,C,E exam) d'insu saidai akwai matsala dan gsky sopy bata wani k'ok'ari,, gashi tasan abubuwa dayawa a exam d'in sai takan kasa rubuta komai akan takardar,, wani sa'in ma haka take fitowa bata rubuta komaiba,, dahaka suka gama rubuta (WAEC) suka fara (NECO) ba laifi Sopy tad'anyi k'ok'ari a neco amma bawani nakuzo ku ganiba,, to sopy ALLAH yabawa mai rabo sa'a dai kawai za'ace.

Suna cikin exam akakai kud'in auren Abdul gidansu fareeda,, sopy tayi matuk'ar farin ciki ,  dan bata san wa fareedan zata auraba,, dukda kullum tana nacin son ganin gwanin fareedar, amma sai tace" mata karta damu zata sansa aranar d'aurin aure,, danshi ba mazaunin kano bane,, ALLAH sarki safiyya itakam ta yarda mijin da fareedan zata aura bad'an kano bane.
    "" dukda har yanzu matsalar rashin zuwan Abdul wajen sopy yana matuk'ar damunta,, amma yanzu takan d'an rage nuna damuwarta agaban mutane dan bata son inna tashiga damuwa akanta, sai idan tashiga d'akine takeshan kukanta, gashi kuma bata iya wani barcin kirki, ALLAH sarki sopy "SO" yanada zafi, musamman ma lokacin da wanda kakeso ke neman kufce maka.

To MASHA ALLAH su sopy sun gama exam, sun shiga kacaniyar shirin bikin fareeda daya rage saura sati biyu,, dan haka yanzu basuda wani lokacin kansu,, amma duk dahaka sopy bata harbo jirgin fareeda da Abdul ba,, dan tuna nintama baitab'a waigawa inda sukeba, bare harta zargesu.

Biki ya kankama sosai, dan jibi d'aurin aure yau kuma kamu,, agidan aunty zainab yayar fareeda suke zaune itama annan rijiyar lemon take, saidai akwai d'annisa tsakaninsu,, suna gidan anata hira da barkwanci irinna k'awaye,, sopy tamik'e tana fad'in kaini barinaje farkon layinnan na siyo gyad'a dafaffa, dan tunda zamu shigo naganta wlhy,, ko akwai mai zuwane???
Kowa yace A'a, fareeda ta mik'e kinga bar 'yan iska K'AWATA  muje narakaki, kuma wlhy ko munsiyo babu maicinta,, fareeda taja hannun sopy suka fita.
        "Suna cikin tfy sopy tace'' sister kinga habibina ko har yanzu baizoba tun wancan satin gashi nima inason muyi maganar aurenmu,, dan nasan kina tfy zan tsani anguwar wlhy.
Fareeda tadafata karki damu sister kibari yau idan munkoma gida saimuje wajensa.
    " sopy tace" toshikenan sister amma wlhy lamarin nan na Abdul yafara isata............tai shiru domin hango Abdul ya doso layin.
Fareeda tace" yaya dai naji kinyi shiru?? Da hannu sopy tanunama fareeda Abdul! Gaban fareeda yay matuk'ar fad'uwa shikuma wannan daga ina?? Fareeda ta fad'a a zuciyarta.
Tofa masu karatun k'a k'a rak'a k'ak'a  kudai biyoni muji mizai farune??? .....................✍🏻



💕Bily💕
💕💕Mrs Abdus'salam💕💕💕
💕I LOVE YOU MY FAN's💕💕
                                            💕
[12/19, 7:24 PM] mrs bilkisu: 11~October ~2016



🔷🔹NI   DA   K'AWATA 🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM 💕




🔶🔸1⃣1⃣🔸🔶


...............fareeda tai saurin cewa  kinga sopy zoki b'uya naje wajansa Dan naji ina zaije ne???
   " sopy tace" gsky ne K'AWATA shawararnan tayi jekiji mizai ce.
Fareeda ta nufi Abdul itakuma sopy ta b'uya.  
Tunda ya hangota yake murmushi,, tak'arasa wajensa da sassarfa tamkar zata kifa,, yay saurin cewa my love! Daga ina??? Tace" A'a kaizan tanbaya daga ina Abdul?? Yace" ni wajenki nazomana.
Tad'an zaro ido waje Abdul miyasa bazaka kirani muhad'u a wani wajenba,, ko ka manta muna tareda sopy anan,, yanzu haka tare muke kuma itace tafara ganinka ma,, sai wayo naimata nace" bari na tanbayeka inazaka??
  " yad'anja tsaki nikam gsky fareeda lamarin nan yafara isata yaza muyita b'oye b'oye akan abinda bashida muhimmanci bayan kuma miji da mata zamu zama,, way ko kina tsoron safiyyane??
  Fareeda ta girgiza kai bawani tsoro Abdul inadai son kozata sani tofa sai bayan an d'aura aurenmu jibi,, yanzu kazo muje kace" mata wajenta kazo dan ALLAH karkayi abinda zaisa sopy ta fahimci wani abu plz kataima keni mijina abin sona!!!!;!! Tafad'a tana matse kwalla,, yay saurin cewa karkiyi kuka amaryata zanyi duk abinda kikeso plz karkiyi kuka.
     "Fareeda tayi murmushi toshike nan muje.

Abdul yazagayo tabayan sopy yace" mai b'uya aii gani naganki.
Sopy tayi saurin juyowa danjin maganar habibinta,, tai murmushi to waya gayamaka ina nan?? Yay d'an murmushi aii basai anfad'a minba zuciyata ma zata iya ganoki,, barema ina kallonku keda fareeda kuna kullawa.
            " sopy tai dariya sosai tace" to naji ina ka kaimin k'awata ne?? Yace" taje sayo muku gyad'a ne, yanzu zata dawo,, tace" okey tokai mike tafe dakaine?? Ya murmusa nazone kawai naganki gimbiyata,, ya d'akko kud'i har dubu goma ya mik'a mata ga wannan kiyi hidimar biki dasuko, saidai kiyi hak'uri babu yawa gashi kuma sunzo miki ak'ure.
Sopy tace" to ngd saidai karage domin kud'in sun yimin yawa, dan mun gama komai,,, Abdul ya girgiza kai kinsan bana son musu kuma babu k'yau maida hannun k'yauta baya.
  Bayanda zatayi dole ta karb'a tai masa godiya.
Ya harareta batare data ganiba azuciyarsa yace" ' yar son banza.
""kud'inda Abdul yabama sopy fareedace tabashi yabata tunda tasan kud'in zasu dawo hannunta ne.

Fareeda tak'araso sukad'an sake tattaunawa sannan Abdul yatafi,, bayan tfyr Abdul suma suka nufi gidan aunty zainab sopy tamik'awa fareeda kud'in my sis ga wannan habibine yabani ki ajiyesu awajenki ko wani abu zai taso mana.
Fareeda tace" ALLAH yasaka masa da alkairi.

RANA BATA K'ARYA SAIDAI UWAR D'IYA TAJI KUNYA:- yaune aka d'aura auren fareeda d'ahiru da Abdullahi Abubakar mai fata,, d'aurin auren dayabawa mutane mamaki, domin mutane dayawa sun san Abdul da k'awar fareeda yake soyayya,, amma gashi yanzu ya auri fareeda, dan danan surutu yafara yawa acikin anguwa.

Su sopy suna makwafta gidan wata saddik'a anan suke zaune,, sopy tagama shirinta cikin ankon dasukayi itada fareeda kawai,, saidai ta manta sark'arta agidansu dan haka tamik'e tana cema fareeda bari ta d'akko,         sopy ta fito tana gaisawa da mutane,, amma sai mamki yakamata dataga anata nunata ana kus kus, bata kawo komai arantaba tayi wucewarta.

Da daddare aka kai fareeda d'akin mijinta dake cikin gidan su Abdul,, dukda darene lamarin yayi matuk'ar bama sopy mamaki,, saikuma gabanta yashiga yawan fad'uwa da sauti da sauri,, bayan raguwar mutane 'yan kai amrya fareeda tacema sopy dan ALLAH ta samomata ruwa tasha,, sopy tace to amrsu ta ango mai dad'in suna aii dole naje neman ruwansha,, bayan fitar sopy fareeda ta d'auki wayarta takira Abdul,, dan dama shitakeson kita shiyyasa ta aiki sopy.

Sopy tana tsaye a k'ofar gidansu Abdul tanata kalle kalle zuciyarta cike da fargaba,, can saitaji muryar adam yana fad'in Abdul kana ganin hakan dakayi shine dai dai tun d'azu nakeson muyi magana kanata min hanya hanya,, yanzu kai kana ganin idan sopy tagano kaine ka auri fareeda mi kake ganin zai farune???
Abdu yay magana cikin tsawa kaga adam kafita hanyata wlhy to miye idan sopyn tagane nine na auri fareeda,, ita uwatace kokuwa zata tsirenine??? 
 Bazata tsirekaba amma tabbas sai ALLAH ya saka mata kuma karubuta ka ajiye ranar nanan zuwa gareku daga kai har fareedar daka aura.

Tun sopy najin abinda suke fad'a harta dainaji,, garin yafara juya mata kafin kace me ta yanke jiki ta fad'e awajan,, dan dana hankalin mutane yadawo gurinta,, Aka fara fad'in "inna lillahi wa inna ilaihirraji un."  Wanine yay k'arfin halin fad'in ad'auketa mana atafi asibiti dan asume take...................✍🏻




💕Bily💕
💕💕Mrs Abdus'salam💕💕💕
💕I LOVE YOU MY FAN's💕💕
                                            💕
[12/19, 7:24 PM] mrs bilkisu: 12~October ~2016



🔷🔹NI  DA  AMINIYATA🔹🔷



NA  BILKISA IBRAHIM💕


Assalamu alaikum masu karatu,, ina mai baku hak'urin canja sunnan wannan book,, domin bansan an rubuta book d'in NI DA K'AWATA  ba sai yanzu,,dan haka yanzu zai koma NI DA AMINIYATA,,, sannan ina k'ara bawa marubuciyar NI DA K'AWATA hak'uri. Ngd acigaba da gashi.  


🔶🔸1⃣2⃣🔸🔶


..............Asibiti mafi kusa aka nufa da sopy,, sannan labari yakai gidansu sopy,,, ALLAH ma yasa uncle kabeer yana nan,, shima yazo d'aurin auren fareeda,, babu b'ata lokaci suma suka nufi asibitin da aka kai sopy,, wadda likitoci suka rufu kanta,, amma ko motsi batayi kwance take tamkar gawa.
     "Ganin dare yafarayi likitoci sukace su inna suje gida abarwa gobe,, aga abinda ALLAH zaiyi kuma,, inna tace" babu inda zataje tananan tareda sopy,, dak'ar aka lallasheta suka tafi akabar uncle kabeer awajenta.

Awannan lokacin kuwa amarya da angonta suna can ana ragargazar amarci,, dan ango bai d'agawa amaryar tasa k'afaba,, dukda yalura tana cikin damuwar abinda yafaru da AMINIYARTA,, itama dai tabada gudummawa dan tasan wannan shine zai k'ara kusanci tsakaninta da Abdul,, zai kuma k'ara zama dalilin da dole iyayensu su barta tazauna tareda mijinta,,, ba k'arya tasha wahala amma ta daure sosai dan tana son Abdul,, to fareeda saimuce ALLAH Yasanya alkairi yakuma shirya masu irin halinku nacin amana da yaudara. Amin

A asibiti kuwa har yanzu sopy bata farfad'oba  kuma likitoci sun dage akan tanada rai bata mutuba,, to ALLAH yasa haka, dan gsky masu karatu indai sopy ta mutu to nimafa 'yar rahoton taku bazan sake kawo muku rahotoba,, ALLAH dai yasa da ranta.
 Shagalin biki yakoma zaman jigum jigum,, dan maman fareeda sai kuka takeyi tana fad'in wlhy saita kashe auren fareeda,, tunda har taci amanar safiyya,, in kuma ba hakaba zata tsinema fareeda inhar bata rabuda Abdul ba. 
      ""Tofa turkashi kunji wata sabuwa masu karatu.""

Har zuwa yamma sopy bata farfad'oba,, dayawa mutane sun fara yarda tama mutu,, dan ko mahaifinta ma cayayi likitoci suyi hak'uri subada gawar safiyya aje amata suttura.
   "Wani likita yace" way baba wayace maka ta rasu?? Yarinyar nan tanada ranta dan ALLAH  kubarmu muyi aikinmu.
 Sai wajen k'arfe 4:46pm sopy ta farfad'o saidai sun hana kowa ganinta,, dansun yimata allurar barci,, saboda ta sami hutu,, dukkan 'yan uwa suna asibitin kowa ka kalla baya cikin walwalarsa,,, labari kuwa sai k'ara baza anguwa yakeyi,, kunsan dai mutane da gulma,, dan yanzu gulma maza da mata kowa ya iyata,, ALLAH dai ya shiryar damu jama'a.

Mahaifin fareeda ya aika hargida aka kira masa Abdul da fareeda,, bayan d'an wani lokaci suka iso,, dukkan dangi sun had'u, mamar fareeda da babanta sai yayunta biyu yaya lawan, da yaya saminu, da zainab, sai k'anin babanta. 
    Sai baban sopy da inna, aunty Nafisa da hauwa'u,, sai uncle kabeer,, fareeda duk tabisu da kallo azuciyar ta tace" tofa wannan gangamin namiye?? Zuciyarta tace mata duk anyishine saboda "k",, tai wani d 'an guntun murmushi aiko sama tarwatsashi dan fad'ansu ko wani hargaginsu bazai tsorataniba,, tuni nashiryama fuskantar wannan matsalar.
 Yaya lawan yadaka mata tsawa to mara kunya idan kin gama yimana kallon rainin arzik'in saiki zauna ko,, mara mutunci kawai.
Fareeda tad'an tab'e baki sannan ta zauna kusada mijinta,, babanta yay gyaran murya, yad'ora da fad'in assalamu alaikum!!! Kowa ya amsa,, yabi fuskokin kowa da kallo sanna yagyara zama yace" Abdullahi!!! Abdul ya amsa kansa ak'asa.
 Baban fareeda yace" miyasa ka auri fareeda bayan kuma da safiyya kuke  tare??? Kuma har munyi maganar aurenka da safiyya harda iyaye aciki??? 
                     Abdul yagyara zama, baba ku gafarceni dacan safiyya nakeso amma yanzu fareeda nakeso kuma gashima har kun auramin ita.
Baba ya k'ara d'aure fuska, to miyasa lokacin da maga batanka suka zo basu fad'i hakaba??? Saima sukace mana yayanka ne zai auri fareedan??
Abdul yace" nine nace sufad'i haka dan karka hanani auren fareeda.
  Baba yaja tsaki to aii har yanzu bata sake zaniba domin dolene kasaki fareeda yanzu anan wurin,,, gaba d'aya wajen saida suka d'ago suna kallon baba banda mama da tace" wannan batu kam tilas ne dole kasaki fareeda ka auri safiyya.
  Baban sopy yay saurin tareta amma dai ba haka mukayi dakaiba malam d'ahiru,, gsky karku raba musu aure.........baban fareeda yay saurin katseshi, saidai kayi hak'uri malam ibrahim nariga nagama yanke hukunci.

Abdul yace" gsky baba saidai kuyi hak'uri wlhy bazan iya rabuwa da matataba ina sonta,, ina kuma burin kasancewa da ita har abada.
  Fareeda ta karb'e wlhy nima baba inason mijina dan ALLAH karku rabamu,,,, aii kafin tarife baki yaya lawan yabata duka jikake taffff,, ta kwalla k'ara tana fad'in wlhy sai ALLAH yasaka min tunda ban yimimaka komai ba mugu azzalumi.......yako tashi yashiga dukanta tako ina,, Abdul yamik'e yashak'i wuyan yaya lawan yana fad'in kai bagidaje mahaukaci wlhy idan hannunka yak'ara sauka akan matata saina kasheka.
Uncle kabeer yadaka ma Abdul tsawa yace" sakeshi,, jikin Abdul yana rawa yasaki yaya lawan yakama hannun fareeda yana fad'in muje gida,,, baban fareeda yamik'e murya a sark'e yace" fareeda inhar kika koma gidan Abdullahi to babuni babuke, nacireki daga cikin 'ya'yana kije nabar masa ke.
            " fareeda tace" baba nasan rankane ab'ace amma wataran zaka gane hikimata ta auren Abdul, harma kayi alfahari da hakan,, mama tace lallai fareeda wuyanki ya isa yanka yanzunan mahaifinki kike fad'ama haka saboda d'a namiji,, fareeda ta tab'e baki mama kema nasan bazaki tab'a ganewaba sainan gaba,, kamar yanda kuka buk'ata zanyi nesa da ku da 'ya'yanku har zuwa lokacin da zaku huce,, aunty zainab dake kusada ita ta wanka mata mari taka'ara mata nabiyu, Abdul yarik'e hannun cikin masiba zainab tace" kaid'an akuya sake min hannu ke kuma wlhy nan bada dad'ewaba zakiyi nadamar abinda kika aikata,, kuma saikinyi mamakin mijin da safiyya zata aura maci amana kawai.
 Fareeda ta tab'e baki wannan kuma bai dameniba,, idan safiyya zata auri mazan duniya bai dameniba tunda nidai nasamu muradina,, taja hannun Abdul suka tafi,, mahaifin fareeda ya yanke jiki yafad'i agurin......................✍🏻





💕Bily💕
💕💕Mrs Abdus'salam💕💕💕
💕I LOVE YOU MY FAN's💕💕
                                            💕
[12/19, 7:24 PM] mrs bilkisu: 13~October ~2016


🔷🔹NI   DA  AMINIYATA🔹🔷


NA BILKISA IBRAHIM 💕




🔶🔸1⃣3⃣🔸🔶


.............gaba d'aya suka nufo kan baba,, uncle kabeer ne yay k'ok'arin yayyafa masa ruwa ya kawo numfashi,, yad'ago yana kallonsu dagaske fareeda tatafi ta zab'i yaron nan sama dani??
 Aunty zainab tace" baba ta tafi kabarta kawai aii "DUNIYA MAKARANTA CE"" yace" shikenan ku shaida nacire fareeda acikin 'ya'yana kuma duk wanda yay mu'amulla da ita acikin ku ban yafe masaba,, kamar yanda ta buk'ata nabarta da Abdullahi.
         Baban safiyya yace" dan ALLAH malam d'ahiru kabar wannan furicin da fareeda da safiyya duk d'ayane agurinmu,, in akayi hak'uri itama safiyyan ALLAH zaibata wani, dama can ALLAH ya rubuta ABDULLAHI mijin fareedane ba safiyyaba......baban fareeda ya k'atseshi malam ibrahim kabarni kawai wlhy nariga na yanke hukunci dan haka kabarni ina ganin mutuncinka.
  Dole kowa yay shiru,, dan sunsan ransa ab'ace yake,, daga nanma kowa yakama gabansa.

Agidan su sopy uncle kabeer yace" wlhy ni abunma ganinsa nake tamkar a mafarki,, dama  akwai iyaye irinna Abdul??
 Baban fareeda yay murmushi abba akwaima wad'anda suka fisu,, ni tun ranar da aka kawo kud'in auren fareeda na fahimci ko mai,, dan haka daga baya na yi bincike,, nagano Abdullahi fareeda zata aura.
 aunty Nafisa tace" amma baba kayi shiru baka fad'awa kowaba??
 Baba yace" hakane Nafisa fad'ar fashida wani amfani, tunda fareedar yakeson aure, dan haka ina mai gargad'inku kada kowa yad'auki wannan abin da zafi,, mutaya safiyya addu'ar samun lfy kawai, dakuma fatan ALLAH yabata miji nagari wanda yafi Abdullahi bawai dukiya nake nufiba,, A'a wanda yafishi k'yawawan halaye.

Kowa ya amsa da to,, yace" kukuma yakamata kushirya kutafi gida jenku,, tunda sunce yau zasu sallamo safiyyar daga asibiti.
  "Suka amsa da to baba"

Da daddare aka sallamo safiyya, koda sukazo gida wanka kawai tayi tasha shayi da magani ta kwanta, dan akwai maganin barci aciki,, baba yace mai sunan baba!! miye likita yace gameda ciwon nata?? Uncle kabeer yaja numfashi,, yaya!! likita yace sopy tasamu matsala a zuciyarta,, dan tadad'e acikin damuwa da yawan fad'uwar gaba,, saikuma fad'uwar datayi shekaran jiya tayitane sakamakon jin abinda bata zataba,, amma yace" idan aka cigaba da lallashinta da yimata abinda zai sakata farinciki to zata dawo kamar yanda take,, inkuma bahakaba zuciyarta zata kamu sosai.
              " inna tafashe da kuka,, ALLAH sarki safiyya kekuma taki jarabawar kenan?? Baba yace" hajara ba kuka zamuyiba addu'a safiyya kawai take buk'ata daga garemu.
 Uncle kabeer yace"gsky ne wannan, nan dai suka cigaba da tattauna matsalar.

Yau da gobe ahankali jikin safiyya yafara sauk'i dan tana samun kulawa wajen baba da inna dakuma uncle kabeer,, yayyen tama suna bata kulawa,, haka mamar fareeda kullum saita shigo dubata itada baban dasu yaya lawan,, jikinta yana yin k'yau saidai yanzu bata son yawan magana,, ko hayaniya, ko fira ake akusada ita saidai kallo,, koda yaushe tana kwance, sallah ce kawai ketashinta abincima bata son ci,, sai uncle kabeer ya lallab'ata.
      " lokuta da dama idan ta tuna cin amanar da AMINIYARTA tayi mata da SAURAYINTA wanda take matuk'ar SO sai kaga hawaye nazuba akumatunta,, takanyi bak'in cikin kub'ucewar mutane biyu masu muhimmanci agareta alokaci d'aya,, sun barta alokacin datake buk'atarsu fiye da kowa,, sun tafi lokacin datake buk'atar abokin shawara,, sun barta lokacin datake buk'atar mai d'ebe mata kewa,, sunyi nisa da ita alokacin datake buk'atar mai share mata hawaye,, tafashe da wani irin kuka mai ban tausayi😭, nima bansan lokacin danawa hawayen suka fara zaryaba, dan nasan zafin rabuwa da masoyi,, saidai nawa mutuwace tarabamu, bakamar na safiyyaba da yana raye yayi nisane da'ita saka makon makircin AMINIYARTA.
          inna tashigo d'akin da sauri danjin kukan safiyya,, ta rungumeta ajikinta tana lallashinta,, haba safiyya kiyarda da k'addara mana alokacin data riskeki,, ki godema ALLAH mana alokacin daya jarabceki,, karki jahilci kanki kiyi hak'uri irin hak'urin manyan ANNABAWA mana ayayinda jarabawa ta riskesu,, inkikai hak'uri sai ALLAH yayi alfahari dake domin yana tare damasu hakuri,, indan kikayi hak'uri sai ALLAH ya musanya miki da mafi alkairi.
 Sopy ta kuma rungume inna tana fad'in to inna zan daina,, kawai abinne yana bani mamaki,, wai fareeda da'ita aka had'a baki wajen cin amanata,, dama tuni tasan dukkan matsalata amma tarufeni,, duk halin k'unci da yawan damuwa dana shiga fareeda tanada masaniya akai,, shiyyasa kullum saitace zataje ta tanbayo miyasa Abdul yadaina zuwa wajena,, kullum da irin tsarin da zata yi min,,, ashe itace kecin dunduniyata ban saniba,, ashe fareedace tushen damuwata tafad'a tana rushewa da kuka,, haba AMINIYATA miyasa kika aikata?? Miyasa kika yimin haka?? Miyasa kika zama mai irin halin muna fukai??? Miyasa saida nayarda dake kikaci amanata??? Miyasa kika zab'i mu rabu akan saurayi???? 
Inna tace" kinga ya isa haka kiyi hak'uri. Sopy ta d'ago tana kallon inna, wlhy inna ba rabuwa da Abdul bane matsalata nafi jin ciwon rabuwa da fareeda,, domin zuciyata da ruhina suna matuk'ar k'aunar fareeda,, itace K'AWA tafarko da zuciyata ta yarda ta ita harta zama AMINIYA mafi soyuwa a zuciyata,, ashe zata rabuda ni akan saurayi,, zata raba tsantsar SO da k'auna da zumincin dake tsakaninmu,, ashe zata saka shakku da fargaba azukata guda biyu da tsantsar yarda ta cikasu??  Ashe duk so da k'aunar dana nunama Abdul da fareeda su babu abinda suka ajiye mini sai tari yaudara da cin amana??? Nikam nayi asarar AMINIYA da miji mafi soyuwa azuciyata,, inna banyi tunanin sake maye gurbin wad'annan mutanen biyuba arayuwata,, domin nayi asarsu alokacin danafi buk'atarsu.
    Inna tace" kiyi hak'uri safiyya ki barma ALLAH shine mai kowa da komai,, inkinyi hak'uri zai musanya miki da wad'anda suka fisu,, kedai ki kasance mai gsky aduk inda kika tsinci kanki,, da ace kekika cutar gara ace ke aka cutar kinjiko???
  Sopy tad'aga kai tana hawaye, insha ALLAHU inna karkiyi shakku akaina,, zan kasance kamar yanda kika buk'ata.
To shikenan yanzu dai ki kwantar da hankalinki kibar yawan damuwa kinga likita yahanki tunani saboda ciwonki,, muma bamu son mu rasaki.
            " to inna zanyi k'ok'ari insha ALLAHU kodan hankalinku ya kwanta.
Inna tayi murmushi to shikenan auta ta.
Sopy tace" inna ina uncle yake??
Yaje siyo miki maganinki yanzu zai dawo,, wlhy inna bana son uncle yatafi yanzu dan ina jin dad'in zama dashi.
To aiko saidai hak'uri auta kinga dole ya koma wajen aikinsa,, dan kinga bikinsa shima yanata gaba towa.
       Sopy tace" hakane kuma inna, ALLAH dai yakaimu lokacin.
Inna tamik'e tana fad'in amin autata.................✍🏻



💕Bily💕 
💕💕Mrs Abdus'salam💕💕💕
💕I LOVE YOU MY FAN's💕💕
                                           💕
[12/19, 7:24 PM] mrs bilkisu: 14~October ~2016



🔷🔹NI   DA  AMINIYATA 🔹🔷




NA BILKISA IBRAHIM 💕



🔶🔸1⃣4⃣🔸🔶


..................Safiyya tasamu sauk'i Dan jikinta yayi k'yau saidai tayi matuk'ar rama,, fuskarta tayi wani fayau,, bata zuwa Ko ina koyaushe tana gida tareda innarta,, uncle kabeer yasaya mata waya mak'yau,, yabud'e mata watsapp da facebook duk dan surink'a d'ebe mata kewa,,, indan baya aiki saisuyita hirarsu a watsapp,, yabama budurwarsa nomber ta,, ta sakata a group's 2  dayawa NA Novels dana hirar duniya dana addini irinsu HANYAR TSIRA  dan wannan gidan bayin ALLAH suna k'aruwa dashi sosai ALLAH yabiya masu tunatar damu aduk inda suke. 
       "" irin wad'annan abubuwane sukan d'auke mata hankali bata samun lokacin tunani,, data ta  wata 1 uncle kabeer ke siya mata,, shiyyasa batada matsalar MB,  saidai takanyi kewar fareeda, Dan tunda suke basu tab'a yin kwana biyu basa tareba,, Dan haka duk kewarta ta addabeta, takan kwaso pictures d'insu taita kallo tana tuna baya,, duk abinda yashafi fareeda sopy ta maidashi wani madubinta,,sai dai idan inna taganta ta gurgiza kai kawai amma tana matuk'ar tausayin 'yar tata.

Su fareeda anata shan amarci,, komai yanata tafiya yanda takeso,, Abdul yana tattalinta komai takeso shi yake mata,, inagama ansamu rabo dan naga tayi wani fari,, kokuwa duk amarcinne oho dai,, mudai 'yan kallone. 

Yau sopy anacikin farin cikin zuwan uncle kabeer,, sai hidimar girka masa abinci takeyi, inna taji dad'in yanda taga tasaki jikinta yau tana walwala, dan tunda abinnan yafaru basa ganin dariyar sopy,
 Amma yau daka kalleta zaka gano farinciki a tareda ita.
     "Sai wajen k'arfe biyu uncle kabeer ya iso, shima yayi farincikin ganin yanda jikin sopy yayi k'yau saidai kawai ramar datayine, tana zaune kusada uncle kabeer dake cin abincin data dafa masa,, takalle sa uncle kana ganin baba zaiyyarda da k'udirinmu kuwa? ?? Uncle kabeer ya ce, "aii dama tunda naga farincikinki ya yauta nasan akan maganar damukayine", karki damu zanyi iya k'ok'arina tayanda zai fahimceni, insha ALLAHU  zai amince.
   Sopy ta ce, "danayi farinciki mai tarin yawa uncle, nasan hakan zaik'ara nisanta zuciyata daga damuwar data tsinci kanta. 
  Uncle kabeer yay murmushi hakane my daughter! Insha ALLAHU nan gaba kad'an komai zai zama labari, kedai kiyi k'ok'arin cika min burina,, dan yanzu zaki shirya muje makarantarku mu amso exam d'inki.  
  Cikin zumud'i ta ce, "angama my dear uncle! Inna dai tanajinsu bata tankaba, dan bata fahimci inda zancen nasu yadosaba.

Sun karb'o sakamakon  jarabawar saidai sopy batayi k'ok'ari a WAEC nataba.
  Uncle kabeer ya ce, "sopy ya akayi haka tafarune??  Sopy tad'an sosa gefen wuyanta, wlhy uncle! Sannan ina cikin wani yanayine!!
  Uncle yay murmushi sannan kina cikin shauk'in son Abdul ko?? "Tasa hanu ta rufe fuskarta tana fad'in "kai uncle".
  Ya ce, "i, mana hakane", amma babu damuwa saimuyi amfani da NECO kawai, dama mun gama magana da abokina,, shima malamine a "B,U,K", nasan zai taimaka mana sosai.
  To uncle nagode sosai ALLAH yabiya ka kaidai!! Yay murmushi  to amin sopy na.

Sai dare uncle kabeer yasamu zama da baba, bayan sun gaisa ya ce, "yaya dama maganar yarinyar nan ne yakawoni.
   Baba ya ce, "wace yarinya kenan?? 
 Uncle yagyara zama, yaya yarinyar dazan aura!
 Baba ya ce, "to miya faru da ita??
Babu komai yaya babanta ne , dama ya rok'eni akan dan ALLAH nabarta ta k'are karatunta, tunda saura shekara d'aya kacal, to nima sainaga hakan zai taimaka minma na k'arasa gidana, amma yaka gani??
   Baba yaja numfashi, to idan haka yafi alkairi ALLAH ya tabbar abba, mudai kullum addu'ar fatan alkairi muke maka, da fatan gamawa lafiya, dan kai yaron kirkine, nak'agu naga ka ajiye iyali kaima.
  Uncle kabeer yay murmushi karka damu yaya insha ALLAH zanyi adai k'ara tayamu da addu'a,, sai dai yaya bayannan inada wata buk'ata awajenka!! Inhar ban takuraka ba?? 
  Baba ya murmusa karka damu mai sunan baba fad'amin buk'atarka indai batafi k'arfinaba zan yi maka ita.
  Uncle ya ce, "batafi k'arfin kaba yaya! " dama dan ALLAH ina son kayarje min namaida safiyya makaranta, dan wannan zaman nata bashida wani amfani, karatu zai matuk'ar taimaka mata wajen mance abubuwan dasuka faru abaya..................✍🏻



💕Bily💕
💕💕Mrs Abdus'salam💕💕💕
💕I LOVE YOU MY FAN's💕💕
                                             💕
[12/19, 7:24 PM] mrs bilkisu: 15~October ~2016



🔷🔹NI   DA  AMINIYATA 🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM 💕



🔶🔸1⃣5⃣🔸🔶


...............Baba yaja numfashi, abba ban katse maka hanzariba, amma da dai anhak'ura da karatunnan hakanan, tunda ansamu na zaman duniya, sai kuma ayi aure.
   Uncle ya ce, "hakane yaya, amma yanzu naga bawani tsayye bane ahannu, amma dazaman banzar gara ace karatu takeyi,, kotana karatun tasamu miji saitayi aurenta.
   Baba ya kalli inna, to hajara kinji abinda abba ya ce, "amma ya kika gani??
  Inna tai dariya, malam nikam banida shakku akan babnmu, dan haka kabashi dama, nima inaga hakan zai taimakawa safiyya wajen mance wasu abubuwan.
   Baba ya ce, "to akira safiyya muji ta bakinta"
Uncle yay murmushi karka damu yaya indai safiyyace mungama magana da'ita.
  To, to, kace dama saida kuka gama shawararku sannan aka tuna damu!  Dariya sosai uncle yakeyi "cikin dariya ya ce, "A'a yaya mu mun isa; nan dai sukayita hirarsu da wasa da dariya.

TUNATARWA:- inaso naja hankalin iyaye akan ilimin 'ya'yansu, mafi yawan iyaye sukan d'auki ilimin 'ya'ya mata ba'abu mai muhimman ciba,, ni anawa ganin ilimin d'iya mace yafi na kowanne muhimmanci, karku manta uwa itake bada tarbiyya, kuma yara suna tashi ne da harshen mahaifiya, kunga kuwa ilimin d'iya mace yanada muhimmanci matuk'a,, dan zata zama foundetion na ilimin 'ya'yanta,, wannanma kad'ai ya isa yazama abu mai muhimmanci ga bawa mace ilimi,, sannan ko a gidan aure zakaga mace mai ilimi tafi kowa iya rik'e miji da tattalinsa,, dan haka mubama 'ya'yanmu mata ilim addini dana zamani,, ALLAH YASA MU GANE.

UNCLE kabeer yanata k'ok'ari wajen nemawa sopy Admission a (BUK ) da taimakon wani abokinsa aka dace,, dakansa yaymata komai.
   To ALHAMDULILLAH komai dai ya kammala,, ranar monday sopy zata fara zuwa makaranta,, 😅dan haka tafi kowa fareenciki,, harta k'agara ranar tazo.

Su dai su inna sunata yima sopy nasiha, akan tazama mace tagari mai rik'e mutuncinta da darajarta,, idan ance 'ya mace taje tayi ilimi, bawai ananufin taje tayi iskanciba,, dan dayawa 'yan uwa mata idan suka samu saken zuwa nema ilimi,, sukan d'auka sun samu wayewa daganan sai afara iskanci,, kaiconmu wlhy 'yan uwana mata, har yanzu wasunmu basu fahimci miye wayewaba dayawanmu muna jahiltar wayewa,, ballagar mace wadda ta maida kanta akuya ba ita bace wayayyiyaba,, wanna itace bagidajiya jahila,, mace mai kamunkai da girman kai awajen maza marasa tarbiyya,, mai adiini itace wayayyiyar mace, kuma suma mazan sunfi sonta,, zakaga duk iskancin namiji da mugun halinsa yana burin auren mace tagari, kodashi bai kasance miji nagariba, to 'yan uwana ya kama ta mu gyara, kodan cin ribar rayuwarmu,  ALLAH dai yasa mugane.
    Su inna dai sunyima sopy nasihohi masu ratsa jiki da zuciya,, sunkuma yimata fatan alkairi da samun nasara arayuwa.
  Saboda yanayin rayuwa,, sai uncle kabeer ya nema mata gurin zama a hostel, dan kar wataran kud'in mota ya gagareta,, itama hakan yayi mata dad'i, dan zaman anguwar yana d'an sata tayita tuna wasu abubuwan,, kuma idan tafita sai mutane suyita kallonta, 

wasuma har nunata sukeyi, to, tasan idan tayi nisa da anguwar zata sake, ta kuma manta da abubuwan dasuka faru abaya. 

Ku kasance dani akoda yaushe, ina muku fatan alkairi ...................✍🏻



💕Bily💕
💕💕Mrs Abdus'salam💕💕💕
💕I LOVE YOU MY FAN's💕💕
                                            💕
16~October ~2016



🔷🔹NI   DA  AMINIYATA 🔹🔷




NA BILKISA  IBRAHIM 💕



🔶🔸1⃣6⃣🔸🔶


.............Sopy ana makaranta, komai yana tafiya yanda takeso, sai dai tak'i sakin jiki da kowacce k'awa, duk da ana nuna mata anabuk'atar yin k'awance da'ita, bakamar wata zaliha, itadai sopy tana burgeta, sai dai sopyn tak'i bata fuskar dazata kusanceta, itakam sopy tana tsoron makirci irin nad'an adam ne, dan wadda ta yarda da ita, ta amincewa ita tafara saka mata shakku game da halayen d'an adam, wannan yasa take nisantar 'yammatan makarantar, sai dai tadage tana fahemtar abinda ake koya musu, kuma yanayin tasiri arayuwarta da kuma alk'awarin data d'aukarwa kanta da uncle kabeer.
     Yau tanada lectures d'in safe, dan haka ta tashi tayi shirinta, cikin siket da riga na atanfa jaa da kore, tad'akko fareen hijjabi har k'asa tasaka, tad'an fesa turare mai sauk'in k'amshi, dukda bawata kwaliya tayiba tayi k'yau, dan sopy tanada k'yau irin wanda in kacika kallonta zai k'ara k'ayatar dakai, dukda bak'ace bak'inta yanada k'yawun kallo, gata da jiki maik'yau, irin wanda mutane sukan kirashi karuwan jiki, dolene idan kaga surar sopy komin ustazan cinka ka k'yasa, dan haka koda yaushe takan sance cikin hijjab, saboda idan har tasaka gyale tafita sai tasamu samari samada goma sunce suna sonta, wasukuma kwarjinin ta yake hanasu furtawa.
  Tafito kafad'arta rataye da jar jakka, tafiya take cikin nutsuwa kanta ak'asa, tad'an kalli agogon hannunta mai sauk'in kud'i, tad'an tab'e bakinta, kai barima nazauna anan tunda munada sauran lokaci.
   Tana nan zaune, saitaga d'alibai nata saurin shiga aji,wasuma harda d'an gudu, ita dai kallonsu takeyi, amma batayi wani yink'urin tashiba, zaliha tak'araso tana fad'in "lallai safiyya kina ganin kowa yana k'ok'arin shiga aji, amma ke kina zaune, yau munada lectures da "uncle G" kuma idan har yariga ki shiga aji tofa "k" bazai barki kishigaba......tak'arasa fad'a tana k'ok'arin tafiya, kafin sopy tace,"wani abu tuni zaliha takai k'ofar class.
  Sopy tamik'e itama tanufi class d'in sai dai kash tana kaiwa ga k'ofar ajin shikuma malamin da zaliha takira uncle G yashiga.
  Sopy ta tsaya cak abakin k'ofa, ta daure ta ce, "malam good morning!
  Saida yay mata wani kallo na rainin hankali, sannan ya ce, "morning! da ganan yaja bakinsa yay shiru.
    Sopy tai tsaye abakin k'ofa domin bai bata izinin shigaba, tana nan tsaye wasu 'yammata suka k'araso suma, d'aya acikinsu ta ce, "A'isha yaukam munzo arashin sa'a uncle G!! yarigamu shiga, wadda aka kira A'isha ta tab'e baki, ki ce, "sarkin 'yan girman kai yashiga, nikam wannan malami bansan miya d'auki kansaba???
  Sopy dai tana tsaye tana jinsu, sai dai zuciyarta cike da tambayoyi, akan toshi wannan malamin wayeshi??? Ita dai yau kwananta hud'u a school d'innan, amma bai tab'a shiga a jinsu ba sai yau, to shikuma waye???? 
  Ta maida kallonta gareshi, yana sanye da wani farin yadi mai laushi, rigar da kad'an ta wuce d'uwawunsa,k'afarsa sanye da bak'in takalmi,hakama hannunsa yana d'aure da bak'in agogo,, idanunsa cikin farin gilas siriri,, dukda dukannin kayan dake jikinsa bawasu masu tsada bane, amma shikam sun zauna dai dai da tsarin halittarsa.
  Dogone amma ba canba, amma tabbas baza'a kirashi gajereba,bak'ine amma mai haske, yanada manyan idanu farare tas, wad'anda saboda haskensu har akan iya ganinsu tacikin kwalbar dake idonsa👓, dan har wani k'yalli sukeyi, kumatunsa zagaye yake da bak'in gashi sid'ik wanda ake kira saje, hakama bakinsa zuwa gemunsa shima zagaye yake da bak'in gashin, kansa babu suma mai yawa dan da'alama yanayin aski saidai ba irin tal tal d'innanba, domin akwai gashi kwance akansa bak'i sid'ik yasha mai sai k'yalli yakeyi, yanada d'an jiki dankuwa baza'a kirashi siririba,amma jikinsa yay masa k'yau.
   Yad'an juyo yana kallon su sopy dake waje, yaji ajikinsa tabbas ana kallonsa, sopy tayi saurin d'auke idonta daga kallonsa, shima saiya d'an tab'e baki yacigaba da bawa d'alibai darasi akan English domin shi malamin turancine.
  Yagama lecture d'insa, harda yin test, yazo fita sopy tamatsa gefe tabashi hanya, ko kallon inda suke baiyiba ya wuce abinsa, d'aya acikin 'yammatan nan uku taja tsaki, kai wannan gay d'in akwai rainin hankali saikace d'an wani da wata.

Bayan fitarsa suka shiga, class suka cigaba da karb'ar sauran darasi.
   Sopy zaune ajikin wata bishiya, tana duba books nata, dan bitar abubuwan da'akai musu, zaliha tazauna a kusada sopy tana fad'in 'yar uwa dama kinanan?? Tun d'azu nake nemanki!!
  Sopy tajuyo tana kallonta, e, ina nan, inad'an yin karatune.
  Hakan yanada k'yau zaliha tafad'a tana murmushi.
   Sopy ta maida kanta bisa karatunta, saikuma ta d'ago ta ce, "yauwa zaliha dan ALLAH bani labari gameda "uncle G" malamin d'azu da safe.
    Zaliha ta gyara xama cikin zumud'i, dan ganin sopy yau takulata,, ta kaikaice tafara zabgo Zance tamkar 'yar jarida.
  Nidai ayanda nasani sunansa malam yuseef  Husain Ahmad, Gurum amma anfi kiransa da uncle G, malamin English ne, mutum ne mai aji, baya son wasa, bakuma ya wasa da kowace d'aliba, dan baya sakarwa kowa fuska, inhar kayi sake yashiga aji kafin kashiga, tofa ranar bakada rabo amasu samun darasinsa.
    Yanada ilimi fiye da tunanin mai hankali, dan ayanda naji, nan makarantar yayi, yafita da face class na Resold dan haka suka d'auke shi aiki, zan iya ce miki iya abinda nasani kenan gameda tarihinsa.
   Tad'anyi dariya k'awata kar dai kema kin kamu da son sa?? dan wlhy rabin 'yammatan makarantar nan duk son sa sukeyi,, harso suke yayi musu magana,, amma shi kam ko kallo basu isheshiba, shiyyasa suke cemasa mai girman kai.
   Sopy ta harareta kekam na lura ke 'yar rainin hankalice,, daga tanbayarki tarihin mutum saiki min fassara, to kuwa idan kinason mu shirya dake kidaina min irin wannan.
  Ganin ran sopy yab'aci, zaliha tashiga bata hak'uri.

Fareeda zaune ta zabga uban tagumi babu abinda yake damunta sai tunanin sopy, ba k'arya tayi missing d'inta, sai dai haryanzu bata tab'aji azuyarta ta cutar da sopynba, bare tayi nadamar Hakan,  Abdul yay kissing d'in kuma tunta, tai saurin juyowa tana kallonsa, ya ce, "miye damuwarki?? Tad'an yatsina fuska ta ce, "sopy nake tunani wlhy nayi missing d'inta my love! 
   Abdul yad'an tab'e baki, yana mik'ewa kinga wannan matsalarki ce, ni yanzuma tashi ki kawo min abinci dan yunwa nakeji wlhy,, fareeda ta harareshi oh hakama zakace matsalata ce??? 
  To inada matsala da damuwarki ne?? Cikin jin haushi fareeda ta ce, "A'a.
   Ya ce, "to, kuma, zakiji haushina??
   Fareeda dai taimasa banza tafice domin kawo masa abinci......................✍🏻



💕Bily💕
💕💕Mrs Abdus'salam💕💕💕
💕I LOVE YOU MY FAN's💕💕
                                            💕

[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 17~October~2016



🔷🔹NI  DA  AMINIYATA🔹🔷



NA  BILKISA IBRAHIM 💕



🔶🔸1⃣7⃣🔸🔶


................yauma duk k'ok'arin sopy nagujema tarkon uncle G!, amma saida ta fad'a, dan kuwa harya shiga aji, tad'an cije leb'enta, dan bak'in ciki, tabishi da kallo yana tsaye gaban allo, yauma cikin manyan kaya sai dai yau shaddace mai ruwan k'asa, d'inkin dai tamkar na ranar, dan rigar itama bata wuce d'uwawun saba, amma yau babu glas.
    Sai da yagama lecture d'insa sannan ya ce, "kowa yashirya yin test, kuma yau har nawaje su shigo.
    Wannan magana tasa tabawa mafi yawan d'aliban mamaki, domin duk yanda kuke dashi inhar yarigaka shiga aji tofa bazaka shigoba, bare idan zayyi test, amma yau dakansa yabuk'aci su shigo.
   Bayan shigowar su sopy da ragowar makararru, ya gabar musu da tanbayoyin.
  A hankali yake takawa cikin class d'in bakajin motsin komai sai takunsa, kowane d'alibi ya duk'ufa wajen aikinsa, k'amshin turarensa duk ya gauraye class d'in, yak'araso dai dai inda sopy take zaune, yazuba mata idanu dan ganin batayi wani yunk'urin rubuta wani abubama.
   Jin antsaya akanta yasata d'agowa, kallon ido cikin ido sukaima juna, sopy tai saurin janye nata idon dan baxata juri kallon saba, jikinta asanyaye tamaida kanta ga takarda.
   Shikam wani abu yaji yasoki kansa harzuwa babban d'anyatsan kafarsa, yarintse ido yabud'e, ya salam yafad'a tare da jan ajiyar zuciya, ya wuce abinsa yana cigaba da zagaye d'alibai dan kar suyi satar amsa.
   Lokacin daya basu yana cika yakarb'e, yafita abinsa.

Zaune yake a offece yana duba takardun jiya, dasu sopy sukayi teat, har yazo kan wata takarda danaga ya kurama ido, yajuyata yak'ara juyawa, sai kuma yak'ara maimaita sunan SAFIYYA IBRAHIM KABEER, tabbas yarinyar ce yafad'a afili, domin lokacin dayake zagaye sunan daya gani akan takardar gaban ta kenan, ya cire gilas d'in idonsa, yakuma murza idon dan tabbatar da abinda yagani shin gskne kokuwa idanunsane suke masa gizo??
  Amma yasan ba gizo bane, domin sopy ita kad'ai tazauna, bare ya ce, "wajen wani ta kwafa".
  Yacigaba da juya takardar yana kallo,, aka kwan kwasa kofar domin neman izinin shigowa.
  Ya ce, " who is that?
Daga can akace nine.
  Yay dariya come in, my gay!. 
Abokinsane malam faruk, shima lecturer ne a makarantar, yabashi hannu suka gaisa, ya kalli takardar hannunsa, my man! lfy naga kanata juya takarda??, ko watace ta ce, "tana sonka??, dan na sanka akwai farin jini."
    Uncle G! Ya kalleshi aii idan wannan nema da sauk'i.
  Malam faruk ya gyara zama to minene yafaru??
  Kasan wani abu?? "A'a saika fad'a,, wato wata yarinya ce tabani mamaki wlhy,  jiya namusu lecture, to sai takasance acikin makararru, yauma haka, amma abinda yabani mamaki nayi musu test , saikuma ta amsa mini komai dai dai, yamik'a masa takardar,  karb'a kagani.
   Malam faruk yakarb'a yana dubawa, ya jin jina kai , lallai wannan yakai ayi mamaki, dukda akwai mutane masu kwazo da kwakwalwa aduniya,, kai kankama abin misaline, dan haka karkai shakku.
  Uncle G! Yad'an tab'e baki yana fad'in hakane abokina.

Sopy suna zaune itada zaliha a kofar wani class, saiga uncle G ! Yafito daga ajin, hannusa d'auke da littatafai, suka gaidashi sau d'aya ya amsa musu, har yad'an gotasu saikuma ya dawo, litta taffan hannunsa ya mik'awa sopy,  cikin muryarsa mai dad'i ya ce, " ki kaimin offece d'ina.
   Cikin rawar murya sopy ta ce, "aii ni bansan offece d'inkaba, yad'an juyo ya kalleta, dan har ya fara tafiya, ki tambaya mana, taji yafad'a ya wuce abunsa.
   Sopy takalli zaliha ta ce, "zaliha plz idan kin sani ki rakani mana? Zaliha ta rik'e hab'a rufani ki sayani sopy, sai dai na nuna miki, dan wlhy bakowa yake shiga wannan offece d'inba.
   Kamar ya bakowaba ? To dan me??
  Saboda maishi baya bari, kinga kina k'ara b'ata lokaci muje na nuna miki.
   Sopy tabita tana mamakin yanda yawancin students a d'in makarantar suke shakkarsa,, dukda school d'in ta kasance university gidan 'yanci.
    Da wannan tunanin tak'arasa offece d'in da zaliha ta nuna mata,, a tunaninta baya nan dan haka ta dannakai kawai abinta batareda neman izinin shigaba,, tai sauri jada baya dan ga nin sa zaune akujerarsa ya d'ora k'afarsa saman tebir d'in gabansa, yana latsa waya.
   Ya d'ago yana kallonta idanunsa sanye cikin glas, cikin rawar murya ta ce, "sorry ser    bansan kana cikiba.
  Baice mata komaiba , sai dai ya nuna mata tebir d'in dake gabansa, alamar ta ajiye.
   Ta ajiye ta juya zata tafi,, sai taji ya ce, "waya baki izinin tafiya?? Ta juyo da sauri tana kallonsa, dan batai zaton da ita yakeba, amma saitaga shima ita yake kallo, tadawo ta tsaya, ya sauke k'afafunsa kasa, ya ce, "bismilla zauna".
     Jikin sopy a sanye ta zauna zuciyarta cike da mamakin wannan irin karfin hali  haka.
 Yakai tsawon minti biyar bai sake bi ta kanta ba yanata latsa wayarsa, saida ya mula Dan kansa, sannan yad'ago yana kallonta ya ce, "SAFIYYA IBRAHIM KABEER ko? 
    Dukda ba yau aka fara kiran cikakken sunantaba kamar haka ,  amma saitaji yau sunan yay mata daban tamkar banata ba,  domin kuwa ya iya fad'ar sunan,, kamarma yafi kowa iyawa ..................✍🏻



💕Bily💕
💕💕Mrs Abdus'salam💕💕💕
💕I LOVE YOU MY FAN's💕💕
[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 18~October ~2016



🔷🔹NI   DA   AMINIYATA🔹🔷



NA  BILKISA IBRAHIM 💕



🔶🔸1⃣8⃣🔸🔶


...............ya ce, "koba "k"!, baceba???
   "Tai saurin fad'in nice ser."
Ya jinjina kai tare da janyo wata takarda yamik'a mata, waye ya rubuta miki wannan????
   Sopy takarb'a tana kallon takardar, test d'in ranarce aii, tad'an gyara zamanta, bawanda yarubuta min nice nayi da kaina. 
    Yad'an tsura mata idanu wannda yasa dole tayi k'asa da kanta domin kunya, shikuma ya murmusa, Karo na farko dana tab'a ganin murmushin sa, yacigaba da kallon takardar Kenan yanzu idan nace ki sake rubuta min zakiyi kamar haka??.
    Sopy ta jin jina kai, ta ce, "insha ALLAHU ser".
  Ya ce, "good", takarda da biro yabata, nabaki minti goma sha biyar.
   Tad'an kalleshi saikuma ta kauda kai, azuciyarta ta ce, "idan kasaba rainawa d'alibanka hankali, to nikam bazan amince ba, taja takardar tana rubuta amsoshin tanbayoyinsa, tagama acikin minti goma.
   Yad'an kalleta cike da mamaki, itama kallonsa take, ya danne mamkinsa dan karta kawo masa raini, ahankali ya furta zaki iya tafiya.
  Sopy ta mik'e batare da ta tanka masaba, ta fice abinta.
  Yabita da kallo afili yafurta miskilanci!!, humm kunji masu karatu shiya manta da nasa miskilancin, ahankali ya kwanta da bayansa ajikin kujerar, hannunsa rik'e da takardar data rubuta yanzu, yaja ajiyar zuciya, ya sumbaci takardar ya lumshe fararen ida nunsa masu suffar ganye.🍃
  Narik'e hab'a dan mamaki, marak'isiyya ta zungureni aunty bily mikenan??? Naja numfashi wlhy nima bansaniba marak'isiyya, saidai musa ido akansa dan gano miye sirrin zuciyarsa,, amma wannan irin subba da yayma takardan nan aii abin tanbayane?? Marakisiyya ta ce, "lallaikam aunty bily.
   Sopy na fitowa zaliha ta tareta, sopy miya faru?? naga kin dad'e, Sopy ta harareta to uwar 'yan son gulma babu komai.
  Plz dan ALLAH ki fad'a min nasan hakanan banza bazaki dad'e a offece d'in uncle G! ba, sopy tai d'an tsaki to bawani abubane test d'in jiya yasani na sake.
   Ban ganeba??
 Sopy tai gaba aii dama ke baki ganewa.
  Zaliha tabiyota tana naci, dole sopy tagaya mata yanda sukayi,, zaliha ta ce, "lallai abin mamaki uncle G! kenan, kya k'ara gani indai shine.

:::::::::::::::::::::::::::::::♡ yau takasance alhamis sopy tana Zaune da 'yar kazaginta zaliha suna duba wani book, gurin akwai yawaytar d'alibai  suna shan iska, k'alilanne suke karatu, domin yawancinsu duk tare suke da samari suna hira, wani gay yak'araso inda suke, yay musu sallama zalihace kawai ta amsa amma sopy ko kallo bai ishetaba kanta yana ga littafai.
   Saurayin ya zauna kusada zaliha, yayinda sopy ta mik'e ta canja gurin zama,, saurayin yabita da kallo, zaliha way yaushe k'awarki zata wayene??
   Zaliha ta tab'e baki babu rana  jamilu! dan ita ra'ayinta daban dana mutane.
Ya jinjina kai yana fad'in tofa, jami'a gidan bankashi.
 Zaliha ta kalleshi ta k'yalk'yace da dariya suka tafa da gayen.
    Sopy dake kallonsu taja tsak'i irin wannan abubuwanne yasa bata sakarma zaliha fuska dan ta kula 'yar komai da ruwanka ce, tamai da kanta ga karatunta.
   D'alibai sunata shan hirar soyayya agurin, sai sopy tazama saniyar ware, dan bata bama kowane saurayi fuskar kusantar taba,, batada abokin hira sai littafi ko waya, saikuma idan sun had'u da zaliha, ko kuma tayi tayin chatting abinta.
   Uncle G! Yabi dukkan d'aliban da kallo cikin bak'in ciki, shikam irin wannan halayyar bata burgeshi, domin aganinsa rashin tarbiyya da kamunkai ne yake kai d'aliban maida makaranta wani lambun masoya, yad'anja tsaki tareda k'ara jingina a jikin motarsa, karaf idanunsa akan sopy dake gefe tana karatu, Yay d'an murmushi gsky tana k'ara burgeshi, dan yanason mace mai kamunkai, da rik'e mutuncin kai, ya lura yarinyar tanada tarbiyya dan baitab'a ganinta da wani saurayiba, ya dad'e yana saka mata ido amma haryanzu baiga wani abun aibu a tareda itaba,, saidai yakula muskilace tafad'a aji.
  Yazo zai wuce duk yawancin d'aliban suka shiga gaidashi,, amma ita hankalinta nakan littatafai, ko kuma tanajinsu tadai sharesune oho.
  Shima ya wuce batareda ya kuma kallontaba.

Haka rayuwa taci gaba da tafiya, karatu yana tafiya yanda sopy ke buk'ata, domin tana fahimtar komai dallah dallah, daga ranar kuma bata k'ara yarda tamakara lecture d'in uncle G! Ba, da duk wani malami,, dan ta zauna ta tsarama kanta lokaci tayanda zai amfaneta harma ya amfani waninta,, matsala d'aya tafara fuskanta shine yanda samarin makarantar suke matsa mata, itakam ayanzu ta tsani halin maza dan tundaga abinda Abdul yay mata tayima maza k'ud'in Goro, tana matuk'ar bak'in cikin namiji ya ce, "yana sonta, amma tana iya bakin k'ok'arinta domin kaucewa dukkan wani namiji, ta maida hankalinta akan karatunta gaba d'aya,, tana kuma k'ok'arin mancewa da abinda ya faru a baya, dukda har yanzu  zuciyarta tana k'aunar fareeda, idan tatunata takanji matuk'ar kewarta da begen ganinta, haka son Abdul yana nan azuciyarta amma tana addu'ar ALLAH ya yaye mata sonsa, yakuma mantar da ita shi.

Su fareeda amare, ana gidan Abdul ana shan amarci, sai dai tana fuskantar matsalar yanayin zaman takewar gidan, gidane mai matuk'ar yawa, wanda yatara iyaye da 'ya'ya da jikoki, ga matan yayyensa suna shiga rayuwarta,, tagayawa Abdul amma yak'i d'aukar wani mataki, ga yaran gidan basuda wata cikakkiyar tarbiyya, dan kwata kwata yaran basa respert d'in na gaba dasu, sun raina yayyensu da matan yayyen.
    Fareeda tafito daga kichin hannunta d'auke da kula, Abdul yashigo ransa ab'ace, tad'anja baya dan ganin yanda yafad'o babu ko sallama, ya wuceta batareda ya ko kalletaba, asanyaye tabishi zuwa d'aki, yana kwance akan gado yarufe fuskarsa da filo, tasa hannu tacire filon tana fad'in my love! bakada lafiya ne???
  Cikin matuk'ar masifa ya ce, "asibiti ne ni.
   Tad'anja baya tana fad'in ALLAH yabaka hak'uri.
 Ya maida kansa yana fad'in kayane nad'e gammo na d'ora miki, yaja tsaki.
   Fareeda ta zauna jagwab saman kujerar madubi, ta rintse idanu tana fad'in na shiga uku kardai ace Abdul zai fara juya min baya, lallai dolene na nemi zuwa gidan aunty sadiya.............✍🏻






💕Bily💕
💕💕Mrs Abdus'salam💕💕💕
💕I LOVE YOU MY FAN's💕💕
[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 19~October ~2016




🔷🔹NI   DA   AMINIYATA🔹🔷



NA  BILKISA IBRAHIM 💕






🔶🔸1⃣9⃣🔸🔶


..............zaliha tak'araso dad'an gudunta, tana fad'in kai sopy shine kika taho kika barni??     Sopy tajuyo tana kallonta,  ato naga ke kwalliyace damuwarki ,  bayan kinsan wannan d'an hayak'in shine zai farayi mana lecture yau.
   Zaliha ta ce, "to muje aii akwaima sauran lokaci.
   Jikin wata bishiya suka zauna kafin lokaci yayi.
 Zaliha ta zunguri sopy, sopy! Sopy!! Ga mutuminki!!.
Sopy ta juyo, waye kuma mutumina? Karaf idanunsu suka had'u a karkashin inuwa d'aya,, tai saurin janye nata dan ganin wajensu ya nufo.
  Wad'anda suke wajen suka shiga gaisheshi, yak'araso cikin tak'ama yana sanye da bak'in wando da jar riga, sai zabga k'amshi yakeyi, sajen nan ya kwanta luf luf akan k'yak'yk'yawar fuskarsa, azuciyar Sopy ta ce, "yaukuma k'ananun kaya aka saka".
 Jin zaliha tana gaidashi sai itama tadawo hayyacinta, ta gaidashi itama ya amsa da lfy, kowa yazuba musu ido, shima ganin haka sai kawai ya wayance da tambayarsu wacece sakina musa?? Zaliha ta ce, "uncle G! Muma bamu santaba, sopy ko bama ta tankaba, yajuya yana tambayar sauran d'aliban dake gurun, suma sukace basu santaba, yajuya yatafi, yana maijin haushin kansa, way sai yaushe yarinyar nan zata fahimci inda nadosa ne?? Ko sotake saina furta mata da bakina ne?? Yad'anja k'aramin tsaki, yarinyar nan miskilancin tafa yayi yawa,   gashi sonta yay masa shigar sauri, batareda ya shiryaba, ya lumshe manyan idanunsa masu suffar ganye🍃, ya salam! Yafad'a tareda fitarda huci daga bakinsa.
    Office yakoma yazauna, yajingina bayansa da kujera, idanunsa a lumshe tamkar mai barci.
  K'ofar aka kwankwasa, ko motsawa baiyiba, saida aka buga sau uku sannan ya ce, "waye"?.
Wata zazzak'ar murya ta ce, "nice!!
Ya d'anja tsaki, ya ce, "kowaye ya shigo, ahankali aka turo k'ofar wata k'yak'yk'yawar yarinya fara tas tashigo.
  Ya ce, "kowaye yafad'i abinda yakawoshi!, cikin rawar murya ta ce, "dama dadynane ya ce, "kazo ku gana idan kasamu lokaci.
 Yabud'e fararen idanunsa wad'anda sukai d'anja ahanlin yanzu, sai dai har yanzu yana kwance a kujerar, yabita da kallon rainin hankali, miya faru yake nemana?
  Ta gyara tsayuwa yanaso kuyi maganane.
  Ya jinjina kai, toki sanar dashi yazo shi yasameni dan bana zuwa gidan kowa, kumama inada ayyukan yi masu yawan gaske.
    Kuma indai akan maganar damukayi dakene, karma yafara zuwa wajena, ke kuma ina mai k'ara gargad'inki akan kifita hanyata, inko bahakaba zan cigaba da b'ata miki rai fiyeda yanda kike tsammani.
  Yanuna mata hanyar fita, zaki iya tafiya dan inada aikin yi.
  Ta marairaice fuska tamkar zatayi ihu, ta ce, "plz uncle G! ka daure muyi magana dan mu fahimci juna, wlhy ina tsananin k'aunarka, ka daure kasoni, nayimaka alk'awarin zan kasance yanda kake buk'ata,  wlhy nayi maka alk'awari.
    Uncle G! Yataso daga kwanciyar dayayi ajikin kujera, yad'an tsura mata idanuwa bahijja!! kamar yanda nafad'a miki tun farko, ba soyayya takawoni makarantar nan ba, bake kad'ai kika tab'a cewa kina sonaba, kuma suma amsar dana baki ita nake basu, ina mai baki shawara daki hak'ura kema kamar yanda suma sauran suka hak'ura,, kuduka bakwa cikin irin matar danake son aura, dan haka ina mai baki shawarar ki sama ranki hak'uri, daga yau kuma karki sake zuwa office d'ina, danni ba'a shigo min office saida dalili, kuma dalilin ma wanda yashafi karatu,musamman ma mata, ya nuna mata hanya zaki iya tafiya.
    Taja numfashi idansu, har sun iya hakura da kai toni tabbas bazan iya rabuwa dakaiba, kaine mutum nafarko dana fara so kuma kaine na k'arshe, zan sanar da mahaifina yazo kamar yanda ka buk'ata, tunda kai kace bazakajeba, tana gama fad'a tafice abinta.
    Shima tsaki yaja, yamik'e yana fad'ar ashe zaki mutu da son nawa kenan, dan har abada bazan sokiba, littatafai ya d'iba yafice shima, dan ya gudanar da lecture.
     Ajinsu sopy yanufa, kamar yanda yasaba haka ya aikata, yahana makararru shiga, babu b'ata lokaci yashiga gudanar da lecture.
    Sopy agaba take zaune, duk d'agowar datayi sai sun had'a ido da uncle G!, dan haka ma saita daina kallon inda yake, amma tanaji ajikinta har yanzu yana kallonta, kamar yanda yasaba yauma ya ce, "zaiyyi test.
   bayan sun gama test yabisu yana karb'a, yazo karb'an na sopy, saida yafaki idon sauran d'aliban sannan ya ajiye mata wata takarda, ya karb'i ta hannunta, da ido ya nuna mata takardar daya ajiyemata, batace komaiba tad'auka kawai.
    Bayan fitarsa kowa yafito, kafin ashiga wata lecture d'in.
   Sopy batabi takan takardar uncle G! ba, dan bata d'auketa dawani muhimman ciba...............✍🏻



💕Bily💕
💕💕Mrs Abdus'salam💕💕💕
💕I LOVE YOU MY FAN's💕💕
[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 20~October~2016


🔷🔹NI  DA  AMINIYATA 🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM 💕



🔶🔸2⃣0⃣🔸🔶


............fareeda al'amura sun fara canja mata, dan yanzu Abdul yafara canja yanayin zaman nasu, ga masifar datake fuskanta wajan ummarsa, dan ummar Abdul masifafface, dukkan matan gidan tsoronta takeji, saboda masifarta.
   Ta kula tunda likita ya ce, "tanada shigar ciki, tafara fuskantar matsala wajen Abdul, yafara nisantarta, Baya yin fira da ita yanzu, bakuma yadamuwa dasu kwana gado d'aya.
   Lamarin yana damunta, gashi yahanata zuwa gidan aunty sadiya, ya karb'e wayarta tuni, yauma tana zaune ta yi tagumi, babu abinda take buk'ata sai nama,, tasan kuma Abdul bazai saya mataba, ga cikin nata mai shegen tsurfa da kwad'ayi, ta cije leb'e hawaye suka zubo mata akumatu, lallai idan har rayuwa tajuya mata baya to kuwa taga ta kanta, dan yanzu batada wanda zata tunkara tasamu sauk'i, aminiyarta tayi mata nisa, nisa kuma mai tarin yawa, tasan yanzu babu wadda sopy ta tsana kamar ita, garashin 'yan uwa, ga rashin iyaye, tafashe da kuka, kuka take tamkar ranta zai fita, nikam na tab'e baki dan wlhy ko kad'an banji tausayin taba, na ce, "ni!, barima natafi wajen k'awata sopy, nagano muku takardar da uncle G! Yabata.

Sopy zaune akatifarta, gabanta kankanace yanke a filet, tad'akko littatafanta tana dubawa, hankalinta akwance, zuwa can tabud'e book d'in data saka takardar uncle G!, madina ta tab'ani yauwa aunty bily tad'akko book d'in data saka takardar nan, ALLAH dai yasa takaranta muji, na ce, "to amin deena!.
     Tana bud'ewa takardar ta fad'o, ta d'auka tana jujjuyawa, dan ta manta kota miye, harta cigaba da karatunta saikuma ta d'akko takardar tana d'an tadubawa.
  Ahankali tabud'e, takardar sai k'amshi takeyi, tad'an murmusa, sannan tafara karantawa kamar haka.

💞Assalamu alaikum. 💞
          Gaisuwa dafatan alkairi, ina fatan wannan takardar zata sameki yayin da kike cikin nutsuwarki.
  Ina buk'atar ganinki a office d'ina gobe idan ALLAH yakaimu, karkuma ki shanyani, ga kuma nomber na nanan, da daddare ki kirani ko kimin filashin, dan ina buk'atar ganin nomber d'inki.
   💚kihuta lafiya💚
Youseef Hussain Ahmad Gurum. {Uncle G!!}.

Sopy ta d'an tab'e baki, lallai kam, saidai kayi hak'uri dan bazan iya aikata ko d'ayaba aciki, takai takardar wajen hancinta tashak'i k'amshi ta lumshe mayan idanunta.
   Madina ta ce, "tofa kodai itama ta kamu ne??
  Na ce, "to madina waye yasani, saidai mucigaba da kallon ikon ALLAH.
  cigaba tayi da karatunta, amma lokaci2 takan kalli takardar tayi murmushi.

..yauma kamar yanda tasaba tashirya tsaf, cikin zani da riga na jan les, tasaka hijjabinta har k'asa, tad'auki jakkarta tafita, kai tsaye aji tanufa dan tanada lecture a dai dai wannan lokacin, bayan sungama karb'ar lecture d'in yawancin d'aliban suka firfito, itakam tana zaune abunta, saida taji zafi yafara isarta sannan ta tashi tafito, dan yau bataga 'yar kazaginnataba wato zaliha, gurin data saba zama tazo tazauna, amma yau ba karatu takeba, waya tad'akko tafa chatin da uncle kabeer, sai faman murmushi takeyi wanda yake k'ara k'awatar da k'yawun fukarta.
    Uncle G!, dake tsaye ajikin wata bishiya yaja ajiyar zuciya tareda lumshe idanu, karfa yarinyar nan ta zautashi, dan wlhy jiya dak'yar ya iya barci, yadad'e yana jiran kiranta, amma har yay barci bata kiraba, yasan kuma takaranata letter d'insa amma tashareshi, tacigaba da harkokinta hankali kwance, shi gashi nan tabarsa cikin damuwa, dan wata irin soyayya yake mata mai tsanani, wadda yake ganin 'yammatan!! dasuke cewa suna sonshi!! tasu soyayyar ta k'aryace, ya rintse ido yabud'esu akanta, wani k'ayataccen murmushi tasaki wannada yasa kumatunta lotsowa, shima saiya murmusa.
   Gaba d'aya yinin yau zaman jiranta yazauna yi, amma batazoba, gashi yau bashida lecture dasu, duk sanda aka kwankwasa k'ofar office d'insa saiyayi tsammanin itace, amma sai anshigo yaga sab'anin hakan, har zuwa yamma batazoba, ya tattara yafita shima cikin damuwa, dan yaso sugana.

Itakam sopy tana sane, amma ta share tacigaba da sabgogin gabanta, tun wajen k'arfe 3:30pm  tagama lectures nata, amma tayi tafiyarta d'aki batareda tabi takan uncle G! ba, duk da tasan yana office yana jiranta, dan duk yau bata gansaba ma.

Yau tsawo kwana biyu da uncle G!, yabama sopy letter domin buk'ar ganinta, dakuma bata izinin kiransa a waya, amma bata aikata ko d'ayaba, dukda abin yana cikin ranta, amma ta danne ta nuna baidameta ba, yauma data kasance juma'a kuma bai shigo musu lecture ba, gashi tana shirin zuwa gida weekend, dan haka tashirya bayan gama lecture karfe 11:15am tayi tafiyarta, lokacinma uncle G! Bai shigo school d'inba.
    Bayan shigowarsa yayta baza idanu dan son ganinta, amma ko alamarta bai ganiba, baimaga k'awartataba zaliha,, shikam baya son tanbaya, dan kar akawo masa raini, dole yahak'ura yabarma monday, dan yaci alwashi ranar monday kobata nemeshiba tofa shi zai nemeta, dan bazai iya rik'e sonta azuciyarsaba, batareda ya sanar da itaba, domin sonta yayma zuciyarsa baban kamu wanda babu yanda za ayi ya iya hak'urin rik'eshi, shima mota yashiga yanufi gida...................✍🏻



💕Bily💕
💕💕Mrs Abdus'salam💕💕💕
💕I LOVE YOU MY FAN's💕💕
[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 21~October~2016




🔷🔹NI  DA  AMINIYATA🔹🔷




NA  BILKISA IBRAHIM 💞



🔶🔸2⃣1⃣🔸🔶

...........safiyya ana gida anashan weekend, inna tayi farincikin ganin yanda sopy ta canja, tasaki jikinta sosai sai dai haryanzu tananan arame, dan bata k'ara k'ibaba.
   Yanzu tarage yawan tunani, tafi maida hankali wajen karatunta, babama yaji dad'in ganinta sosai.
    Taje tagaida maman su fareeda, harma tatayata wasu ayyukan, maman fareeda tanata k'ara lallashinta akan abinda yafaru, sopy ta ce, "wlhy mama ni yawuce awajena, dama can ALLAH yarubuta Abdul mijin fareeda ne, dan haka kudaina ganin laifinta, kud'auka wannan yana cikin k'addarar rayuwarmu ne kawai.
    Mama ta ce, "hummm safiyya kenan ke dai mai hak'urice kawai!! Kuma insha ALLAH saikin sami miji nagari wanda yafi Abdullahi k'yawawan halaye, itakam mun barta da wayonta!!.
   A'a mama dan ALLAH karkuce haka wlhy har yanzu ina k'aunar fareeda bana son iyayenmu suyi fushi da ita!!, dan ALLAH kuyafe mata!!.
   Mama ta tsurama sopy idanu, tana matukar k'aunar yarinyar, saboda hak'urinta ga nutsuwa, lallai d'iyarta tayi asara, tunda har tarabuda safiyya bata koyi k'yawawan halaye daga garetaba.
   Nan dai sukaita hirarsu har yamma.
   Tayi k'ok'ari taje gidan aunty Nafisa da auty hauwa'u, har gidan aunty zainab yayar fareeda, nanama hak'uri tayita bata, sopy ta ce, " bakomai yawuce".
   Ranar lahadi uncle kabeer yazo gidan dan shine zai maidata school, ya d'auketa sukaje yayo mata sayya ta kayan provision da Duk abunda zata buk'ata, 'yar gatan uncle kabeer kenan, har d'unkuna yaymata yasaya mata takalma da hijja bai, da yamma tashirya suka tafi, harda kukan rabuwa da inna da baba.
     Amota uncle kabeer! ke tambayarta taje gidan fareeda!? ta ce,:"haba uncle ALLAH ya kiyaeye aii har abada bazanje gidan fareeda ba, saidai idan tazo anguwar magaisa amma bazanje gidantaba!!.
   Uncle kabeer yay murmushi saboda kishi??? Tai saurin fad'in uncle aii ni! Har abada bazanyi kishi da fareeda ba, koda d'imma ina bak'in cikin sub'ucewarta daga garenine, da kuma abunda ta aikata saboda son zuciya, amma ni yanzu haka na yafe mata, sai dai kuma bazamu tab'a komawa kamar daba, dan yanzu banida aminiyar data wuce inna da baba, sai uncle kabeer da my auntys d'ina.
   Uncle kabeer yay dariya to shikenan kema ALLAH yabaki miji nagari.
  Sopy tasa hannu tarufe fuskarta saboda kunya.
  Adai dai wannan lokacinne kuma suka iso cikin makarantar, yasamu guri yay parking, ya zaro waya bari nakira abokina yazo yataremu.
   Sopy ta ce, "waini waye wannan abokin nakane uncle?? Ni tunda nazo school d'innan ban sanshiba.
  Ya ce, "zaki gansa yanzu nan.

Cikin 'yan mintina ya iso, hankalin sopy yana kan waya tana chatin, uncle kabeer yabud'e motar yafito, suka rungume juna shida abokin nasa.
   Kai abokina nazata makarantar nan zata zama gurin zuwanka fiye da haka, amma sainaga sab'anin haka, indai har bawani abu bane yakawoka ba, ba'a ganinka.
   Uncle kabeer yay dariya karka damu indai nine yanzu zaka rink'a ganina sosai tunda my daughter d'ina tana school d'in!!.
   Ya ce, "gsky ne, aii nima yakamata yau nasan wannan d'iyar tamu.
   Uncle kabeer ya ce, "aii gata nan amota ma ita nakawo!! 
   Malamin yay dariya to ta fito, saimu k'arasa office ko?? Murnar ganinka tasa na manta a inda muke tsaye.
   Uncle kabeer ya ce, "sopy tafito ga abokin nasa.
  Da zumud'inta tafito kuwa, tayi turus tana kallon abokin na uncle kabeer,, ba wani bane illa uncle G!, shima kallonta yakeyi cikin wani yanayi mai wutar fassara,, uncle kabeer! Yay dariya to da alama kumma san juna kenan?.
   Uncle G! Yay murmushi, ai d'aliba tace, kaga duk laifinkane kenan???. Uncle kabeer ya ce, "to, kayi hak'uri, ranar dana kawota ina sauri natafi wajen aikine wlhy.
  Sopy ta daure ta ce, "uncle good evening!.
  Ya ce, "ya weekend??
 Ta ce, "ALHAMDULILLAHI.
MASHA ALLAH yafad'a yana kama hannun uncle kabeer!, abokina muje ciki ko.
   Sopy ta ce, "uncle bari nakai kayan d'aki saina dawo muyi sallama, sannan kun gama.
   Okey to shikenan babu damuwa, jeki kai, amma kisamu wasu sutayaki, dan kayan sunyi miki nauyi.
  To uncle!.

Sopy takira zaliha awaya sukazo itada wata k'awar zalihar, suka tayata kwashe kayan, saidai gaba d'aya zuciyaryata cike take da tunanin dama uncle G! Shine abokin uncle kabeer??, k'in fita tayi har saida uncle kabeer ya kirata a waya sannan tafito.
    Bayanda zatayi dole tanufi office d'in dan uncle kabeer ya ce, "tasameshi a can.
 Ahankali ta tura k'ofar office d'in tashiga, office d'in sai tashin k'amshi yakeyi, uncle kabeer ya nuna mata kujerar dake kallonsa tazauna.
   Ya ce, "kindai gama ko?? Ta d'aga kai alamar e, ya ce,"masha ALLAH, yagara zama to sopy! Ga abokina malam youseef tare mukai school d'innan dashi, amma dayake shi abincinsa anan yake, to gashi yana aiki anan, munsha gwagwarmayar rayuwa tare, komai namu tarene a school d'innan, gashinan duk abinda kike buk'ata to kizo wajensa ki karb'a, kokuma idan wani abu yashige miki duhu a b'angaren karatu, to kizo zai warware miki, domin wannan dakike gani kwarone, uncle yafad'a yana kallon uncle G!.
   Uncle G! Yay dariya kaidai masherancine abokina har yanzu kana nan baka canjaba ko?
  Uncle kabeer ya ce, "aii gsky ce, uncle kabeer yacigaba dafad'in abokina ga d'iyata wadda nafiji da ita acikin 'ya'yana, batada damuwa kamar yada nasanar maka, itama tanada kwakwalwar karatu, dan haka ka taimaka mini wajan cika mini kwakwalwarta da karatu.
     Uncle G! yataso daga kwanciyar dayayi ajikin kujera, yad'an tsurama sopy idanu tai saurin janye idanunta daga kallon datake masa, yay d'an murmushi, babu damuwa abokina nakarb'a, ainima d'iyatace.
   Sopy tana mamakin yanda taga uncle G! yanata fara'a yau, domin yau itace rana tafarko dataga murmushinsa, sannan duk d'agowar datayi saita kamashi yana kallonta.
   Sun d'an dad'e suna hira, kafin uncle kabeer ya tafi,  saida suka rakashi har wajen motarsa bayan ficewarsa daga cikin makarantar uncle G! Ya juyo yana kallon sopy, tai kasa da kai dan tasan batada gsky....................✍🏻





💕Bily💕 
💕💕Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 22~October~2016



🔷🔹NI DA AMINIYATA!!! 🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM 💞



🔶🔸2⃣2⃣🔸🔶

...............yagara tsayuwar sa,  aii dole kiji kunya, dan kinsan kinyi laifi.
    Sopy tad'an d'ago ta kalleshi, ganin ita yake kallo yasata saurin yin k'asa da kai, ta daure ta ce, "laifin mi nayi??
  Ya jin jina kai, okey tunda baki d'auki abinda kika aikata amatsayin laifiba shikena, ya kalli agogon hannunsa, yanzu inada wani aiki, amma zuwa gobe zan jiraki a office, kinada lecture d'in safene???
   Sopy ta amsa da e, inadashi.
Okey to karfe nawa zaki fito??
Tayi d'an jim alamar tunani, karfe sha biyu.
  Okey bada muwa, jan jiraki k'arfe hud'u, yajuya yana kallon yanda wasu tsurarin d'alibai masu dawowa weekend damasu harkokin gabansu, dayawansu su suke kallo, yad'an girgiza kai, kinga kije d'aki amma karki shanyani, inko bahakaba to zanzo har ajinku gaban kowa muyi magana.
    Ta zaro ido😳 waje.
yay murmushi kina mamakine ?? To indai hakane kik'i zuwa kigani, saidai kawai ki ganni.
  Ina saurarenki, yafad'a yana tafiya.
    Sopy tabishi da kallon mamaki, wai mutum mai aji da nuna isa, mai ilimi wanda 'yammatan!  da samarin! university ke son yay musu magana,  shine yau agabana, yake buk'atar naje wajensa, tad'anyi murmushi mai k'ayatarwa tanufi hostel.
   D'aliban dasuka gansu aka d'auki gulma zuwa hostel, wasu kuma ganinsu harda uncle kabeer saiba su kawo komaiba aransu, to ALLAH yashiryi magulmata dai.

Washe gari sopy tanata harkokinta, dukda gargad'in da uncle G! yay mata baisa tayi yink'urin zuwa office d'insaba.
   Shikam gaba d'aya hakalinsa yana kanta, karfe d'aya da 'yan muntina yashigo musu lecture,  saboda shi tak'i zama gaba, amma wannan bai hana idonsa lalibota ba.
  Zaliha ta ce, "sopy wai kin kula da kallon da uncle G! Yake miki kuwa, wlhy tun d'azu hankalinsa yana kanki.
   Sopy ta harareta, to uwar magul mata, ke bama karatun kike saurareba, wanda yake kallone agabanki, ni kibarni naji karatu, tana d'agowa suka had'a ido kuwa, tai surin kauda kai gefe.
   Yagama lecture nasa yafita.

Har k'arfe hud'u tayi sopy batada niyyar zuwa office d'in uncle G!, tanata harkokinta abinta, suna zaune itada Nadiya, tana koya mata wani aiki.
    Nadiya ta ce, "kai sopy kekam kin more wlhy, ina son mutum mai kwakwalwa arayuwata, wannan yana d'aya daga cikin abinda yasa kike matuk'ar birgeni.
    Sopy tayi murmushi kekam Nadiya kinada yawan tsokana.
   Nadiya ta ce, "wlhy babu wani tsokana gsky ce nake fad'a, kuma kema kin sani, saidai ki godema ALLAH.
   Kafin sopy tayi magana wani saurayi ya k'araso wajen, ya ce, "waye safiyya ibrahim kabeer!!? Sopy ta amsa da nice, ALLAH yasa lafiya?? Saurayin ya ce, "lafiya k'alau, dama uncle G! ne ya ce, "kizo yana office d'insa, sopy tad'anja tsaki sannan ta ce,"to ina zuwa.
   Aii kije kawai danni ba komawa zanyi office d'inba.
  Nadiya ta ce, "kitashi kije bakisan miya faruba, badan tasoba ta mik'e tanufi office d'insa.
    Saurayin ya kalli Nadiya, Nadiya dan ALLAH uncke G! Surayin yarinyar nan ne??
   Nadiya ta girgiza kai, A'a, ba saurayinta bane, amma nima bansan dalilin dayasa yake nemanta ba, amma kai miyasa ka tanbaya?
   Naje wajensane, shine ya ce, "nakira masa safiyya ibrahim, toni abunne yabani mamaki, danshi bai cika kula matan makarantar nan ba.
  To babu abinda yake tsakaninsu, kuma maza dai kunzama magulmata.
  A'a bawani gulma daga tambaya?.
  To miye na tambayar, shin uncle G! Ba mutum bane, koko shi bazai iya yin soyayyaba ne?? Inma hakane wlhy nikam zanyi farinciki.
    Saurayin yay dariya aii munga shi baya kula mata, gashi kuma kun mutu asonsa, kamar makarantar nan babu wani namiji sai uncle G!, bakuda wata hira sai tashi, komai uncle G!, tamkar wanda aka halitta da gold.
   Nadiya ta ce, "yanada kamun kaine, ya iya rik'e mutuncin kansa fiyeda sauran malaman da d'alibai, baya wasa da kowa, gashi kuma mai aji da ilimi.
   Saurayin yay gaba dan jin haushin furicinta.

Safiyya ta nufi office d'in uncle G!, saida taje k'ofar takasa shiga, tadad'e a tsaye, dan takasa kwankwasawa, ganin wasu d'alibai suna kallonta yasa ta daure ta kwankwasa ahankali batayi zaton zaijitaba ma, amma sai taji ya ce, "yes come in.
   Ta d'auki tsawon minti biyu bata shigaba, ganin batada fafita yasa ta tura k'ofar office d'in tashiga, wani k'amshi ne yadaki hancinta, tashak'a tad'an lumshe idanu.
   Cikin muryarsa mai dad'i ya ce, "shigo mana".
   Cikin sanyin jiki ta ida shigowa ta maida k'ofar ta rufe,, ta jingina da k'ofar.
  Yana zaune a kujerarsa, gabansa da tarin takardu, yana dubawa inaga namasu test ne, dan ya kware wajen yima d'alibai test, jin anyi shiru yasashi d'agowa, azatonsa komawa tayi, amma saiya ganta atsaye, tana kallonsa, ya ce bismilla zoki zauna.
  Ganin fuskarsa babu walwala yasa ta k'arasa ta zauna a d'aya daga kujerun dake gaban tebir d'in gabansa, yacigaba da duba takardun gabansa, batareda yakuma bi takan taba, yad'auki tsawon minti bakwai, kafin yad'an d'ago ya kalleta, tana zaune kanta ak'asa tana wasada wani zobe dake yatsanta na biyu, yad'anja numfashi sannan ya maida kansa ga aikinsa.
    Cikin muryarsa mai amo da taushi ya ce, "yauma da bansa a nemomin keba da bazaki zoba ko?? Yacigaba da fad'in babu k'yau sab'a alk'awari dai.
    Sopy ta ce, " azuciyarta aii ni ban maka alk'awarin komaiba,, amma afili saita te ce, "aii dama zanzo.
  Ya ce, "aii koma bakizoba ni zanje nemanki, dan na matsu muyi magana, tad'ago tana kallonsa, yana duba takardunne yana maganar.
    Yad'ago zai mata magana, tayi saurin maida kanta k'asa, ya murmusa, tareda mik'ewa yanufi inda take, d'ayar kujerar dake kallonta ya zauna, k'amshinsa ya yawaita agurin, yay gyaran murya tare da fad'in kinsan abinda yasa nake nemanki??.
   "Ta girgiza kai"
 Yad'ora kafarsa d'aya saman d'aya, ya kwantar da bayansa ajikin kujerar,, saida yay mata kallon mintina uku sannan yaja numfashi, ina son na tambayeki samarinki nawa???.
   Da sauri sopy tad'ago tana kallonsa, amma saiya gimtse fuska dan baya son raini.
  Ta maida kanta k'asa tana cigaba da lankwasa yatsun hannunta suna k'ara.
   Ya ce, "ina sararenki!!.
Sopy ta daure ta ce, "ni fa banida saurayi, cikin shagwab'a tayi maganar.
   Yay murmushi tareda fad'in masha ALLAHU, yakuma ce wa," to yaushe kika shirya yin Saurayin?, nanma saida ta kalleshi sannan ta ce, "banda lokacin aikata hakan.
  Nanma saida ya murmusa, ya ce, "masha ALLAHU, yataso daga kwanciyar dayayi, ya ce, "toni na shirya yin auren safiyya, domin matata tarigaya ta iso, ba wasa nazo dashiba, domin inda buk'atar yin aure yanzu, yaya kenan??.
  Sopy ta ce, "a zuciyarta, to ni ina ruwana da shirya yin aurenka ne??
   Yaci gaba dafad'in nina shirya kefa?? Dan inason muyi aure ba soyayyaba, idan kinje gidana zan nuna miki dukkan soyayyata.
   Sopy ta ce, "ban ganeba??
Ya murmusa zaki gane nan bada dad'ewaba, kije kiyi tunani akaina, kabeer yasanar dani komai daya shafi rayuwarki, dan haka bakida matsalar yimin bayanin kanki, nakuma yimiki alk'awarin mantar dake abinda yafaru dake abaya, sannan daga yau karna sake ganinki da zaliha, dan batada tarbiya, nasan bak'ya kula samarin  makarantar nan, to karki fara domin inada kishi mai tsanani, zan iya komai yayinda naga abinda zai tada min kishina, ya mik'a mata wani littafi mai d'an girma, ga wannan ki karanta lokacin dakika samu dama, zaki samu dukkan abinda ya danganceni acikinsa, dukkan tarihina yana nan.
    Tasa hannu biyu ta karb'a, ya d'akko lemon dake saman tebir d'in ya mik'a mata, sorry ga wannan kisha!.
  Ta girgiza kai A'a nagode.
Ya ce, "kina nufin bazaki shaba, ko kina kyankyamin abin hannuna ne??.
   Tai saurin girgiza kai, ya ce, "to karb'a kisha, ta ce, "aii ina azumine.
Ya ce, "wow nice, azumin me kenan??, ta ce, "na nafila.
   Ya kuma cewa nice, aii haka akeso, to idan kinsha ruwa wace addu'a zakiyi akan aurenmu?.
     Ta k'ara k'asa da kai, batareda tayi maganaba.
    Ya ce, "kunyarki tayi yawa, amma zsn rage miki ita, dan dama haka nakeson matata ta kasance mai tarin kunya da nutsuwa, gashi ALLAH ya kawo min alokacin danake tsananin buk'ar hakan, wannan week d'in zanje gida nasanarda iyayena nasan zasuyi matuk'ar farinciki, dan kullum burinsu kenan, gashi dama sunsan kabeer, dan haka ki zauna da shirin zama matata nanda k'arshen shekara 2016.
   Tayi saurin kallonsa, ya kashe mata ido d'aya, ina fatan kin shirya salo salo na soyayyar dazaki nuna min, danni mutumne mai buk'atar a soshi da nuna min tattali yak'arasa fad'a a hankali.
    Itadai sopy takasa koda k'yak'yk'yawan motsi, dan ita mamaki ma yake bata, ko ina miskilancin da jan ajin nasa?? Dama yana magana haka??.
    Kamar yasan tunanin datakeyi, ya ce, "kina mamakina ko? To daga yau kibari, domin ni mijinkine, ina fatan  kwaykwayon {MANZON ALLAH S A W} ne, domin ya nunama mana yanda zamu so matanmu da kuma yanda zamu zauna dasu, dan haka kinada matuk'ar aiki agabanki,, ki shirya kuma.
    Ya d'auki wayarta dake kan cinyarta, nomber d'insa yasa yakira wayarsa, sai kuma yacigaba da binciken wayar, babu wani abu mara k'yau aciki, saima hotu nanta masu k'yau, yagama gani ya mik'a mata.
     Ta ce, "bari natafi kar mutane su zargi wani abu.
   Ya gyara zama karki damu dasu, danni basu bane agabana, amma duk da haka na fahimceki, nima bana buk'atar kowa yasan wannan maganar sai an gama komai, kinji ko.
   Ta jinjina kai alamar to.
 Ya ce, "to tashi kije dan yamma tayi, sainazo barka da shan ruwa....
Aii kafin yarufe baki tayi waje.
   Ya kwanta ajikin kujerar, ya lumshe idanu yana murmushi, ya ce, "ya ALLAH ka mallaka min wannan baiwa taka mai tarin nutsuwa da addini.
    "muda muke a lab'e, ni da su pii pii mukace amin ya Rabbi.....................✍🏻




💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 23~October ~2016




🔷🔹NI DA  AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💞





🔶🔸2⃣3⃣🔸🔶

..........kwance take bayan ta gama shanruwa, tayi zugum dan kuwa tana duniyar tunanin abinda yafaru d'azu, tsakaninta da uncle G!, ta tuna yanda yake magana cikin gadara da bada umarni.
    "Toni na shirya yin aure safiyya, domin matata tarigaya ta iso, bawasa nazo dashiba, domin inada buk'atar yin aure yanzu,"
    Tayi murmushi, tareda sake tuno wata maganar tasa.
 "Dan inason muyi aure ba soyayyaba, idan kinje gidana zan nuna miki dukkanin soyayyata".
  Taja numfashi tareda gyara kwanciya, wato shi baya lallashi, kai tsaye yake magana babu wani kwala kwala, to amma shi baisan ba'a umarni a soyayyaba ne?.
  Ta tuna inda yake fad'in, daga yau karna sake ganinki da zaliha dan batada tarbiyya, nasan bakya kula samarin makarantar nan, to karki fara domin inada kishi mai tsanani, zan iya komai yayinda naga abinda zai tada min kishina".
    Ta murmusa, su uncle G! Masu kishi, to ina ruwana da kishinka, ni nan dakake gani maza duk d'aya na d'aukeku, a kan mizani d'aya nasakaku, taja ajiyar zuciya domin jin an kwala kiran sallar isha'i, tamik'e domin gabatar da sallah.
    Saida ta kammala komai na al'adar rayuwarta, sannan tazauna domin duba book d'in da uncle G! Yabata, ga gajiyar azumi, tazauna tana fad'in wash ALLAH!! aii duk gajiyar danayi bazata hanani karanta book d'innan ba, tai saurin kallon wayarta datake wringing sabuwar nomber ce, dan haka ta share, saida aka k'ara kira sannan tad'auka tana mita, tai shiru batareda ta amsa ba, daga camma ank'iyin magana.
   Ta daure ta ce, "kowaye idan bazaiyyi maganaba tofa zan kashe".
   jitai wata sassanyar murya ta ce, "assalamu aliki?.
   Sopy taja ajiyar zuciya domin tagane mai maganar, ta amsa da wa'alaikassalam, ta d'ora da fad'in good evening sir.
   Yay murmushi mai sauti, ya ce, " evening, kinsha ruwa lafiya?
   "Lafi law, sopy tafad'a"
Ya ce, "masha ALLAH", Amma a canja min wannan sir!! D'in.
   Tai d'an murmushi, to aii kai malaminane, in bance maka sir!! Ba mixan ce maka?
  Ya ce, "hummm, ga sunaye nan masu yawa, darling, honey, dear, my love, prince, gasunan dai dayawa.
   Hannu tasa ta rufe fuska tamkar yana gabanta.
   Jin tayi shiru yasashi fad'in ya dai?
  Nanma shiru tayi.
Ya ce, "okey, sarkin kunya, amma yakamata arage kunyarnan ko? Dan zata d'an cutar dani, in tambayeki mana??
   Ta ce, "to, tambayeni?
  Okey ince dai kinyi mana addu'a?? yayinda zaki sha ruwa, dan kinsan ana karb'ar addu'a a irin wannan lokacin.
   Sopy ta gyara zama, ta ce, "e, nayi.
  To, mikika rok'ar mana?.
"Komaima, na rok'a" sopy tafad'a, asanyaye. 
    Ya ce, "nice, "to d'an fad'amin mana naji.
  Cikin shagwab'a ta ce, "ni dai basaina fad'aba.
  Uncle G! Yay dariya, ya ce, "nice, my sopy karki damu wataran zaki fad'a, bari nabarki kiyi barci, goodnight.
  Kafin ta ce, "wani abu ya sumbaci wayar, ya kashe, sopy ta rintse idanu tabud'e, ya salam ta fad'a tana kwanciya, dama maza basuda kunya, duk jan ajinsu dawani jijida kai, idan akazo fagen soyayya saisu canaja, duba dai kiga uncle G!, ni wlhy mamakima yake bani, ta lumshe ido tana murmushi, wanda itama batasan dalilin saba.
   Ta dafe k'irjinta tana fad'in oh ni safiyya, waiy mike shirin faruwa dannine?? Miyasa nike shiga farinciki aduk lokacin da uncle G! Ya kasance danine?? Idan ban ganshiba nakanyi kewarsa? Shin miye dalilin hakan??.
   Zuciyarta ta ce, "kin kamu da sonsa ne.
   Ta girgiza kai tana fad'in ban yardaba, alokacin dana keson Abdul bahaka nakejiba aii, akwai dai dalili, to amma miye dalilin??
   Uncle G! Yana burgenine kawai, amma bawai ina sonsa bane, zan iya cewama har yanzu ban amince da batunsa na d'azuba, domin kuwa Abdul yasa nayima dukkan maza kud'in goro a fannin yaudara, bana tunani zan sake shiga tarkon son wani namiji ahalin yanzu, nariga na shafe babin soyayyar wani namiji arayuwata, nasan ban isa nace, "bazanyi aureba, tunda nima saida akayi aure aka haifeni, amma koda nayi aure mijin dana aura bazai samu wata soyayya agareniba, sai dai kuma bazan iya nuna hakan ga uncle G! ba, saboda yanada girma a idona, malaminane abokin uncle d'inane, sannan koba komai ya girmeni, ta jawo book d'in domin karantawa.
   Kubiyoni masu karatu, dominjin tarihin, youseef hussain Ahmad, wato uncle G!!!....................✍🏻




💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 24~October~2016



🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM 💞



🔶🔸2⃣4⃣🔸🔶

.............TARIHIN UNCLE G!!!.
uncle G!, kona ce youseef hussain Ahmad, d'an asalin garin gurum ne, a k'aramar hukumar tsanyawa.
   Malam hussain shine mahaifinsa, suna kiransa da baba, sahura itace  mahaifiyarsa suna kiranta da gwaggo, su hud'u iyayensu suka haifa, hafsat itace babba tana aure anan cikin gurum harda yaranta, yusif shine nabiyu uncle G! Kenan, sai Libabatu itama tayi aure tanada yara,  sai auta Aysha tana karatu yanzu tana (jss, a secondary ).
    Gidan su uncle G! Talakawane sosai, saidai mahaifinsu yana son karatun boko sosai, wannan yasa ya tsayama 'ya'yansa sukai karatu, duk da matan daga secondary ake musu aure, amma sun tsayama uncle G! Yayi karatu mai zurfi, dukda kwakwalwarsa ta taimaka masa wajen kaiwa ga matakin dayake a yanzu, bak'aramar gwagwar maya akashaba wajen karatun uncle G!, amma idan ALLAH ya ce, "kaine tofa kaine".
   Bayan ya kammala deploma d'insa ya samu aiki a primary school d'in Gurum, wannan ma ya taimaka masa wajen cigaban karatunsa, dan yana koyarwa ya rubuta takardar izinin komawa k'aro ilimi, da taimakon wani bawan ALLAH yasamu shiga (Ado bayaro university kano) anan ne ALLAH Yahad'ashi da uncle kabeer, duk talaucin gidansu sopy! Sunfi su uncle G! Arzik'i, dan haka uncle kabeer yataka rawa mai yawa arayuwar uncle G!, tab'angaren kud'i da wasu abubuwan, sun shaku da juna sosai shida uncle kabeer.
    Uncle G! Bashida aure, dukda iyayensa suna damuwa da zamansa haka, akullum yana fad'a musu aure lokacine idan lokacin yayi zaiyi aure, yaso auren wata yarinya anan cikin garin gurum, amma sai ALLAH ya d'auke kayansa tarasu tunda ga nan bai sake yink'urin aureba sai yanzu dayaga sopy.
   Uncle G! Yazama wani tauraro mai haskawa agarinsu, dan mutumne mai girmama manya, dakuma son cigaban matasa, har k'ungiyar taimakon matasa gareshi a k'auyensu, dukda bawani kud'ine dashiba saidai rufin asirin ALLAH,
  Wannan shine tarihin uncle G!, atak'aice, nan gaba zaku rink'a jin sauran bayani akansa.

Sopy taja ajiyar zuciya, fuskarta d'auke da murmushi, lallai uncle G!, Ansha gwagwar mayar rayuwa, gsky yabata tausayi, dama ance babu maraya sai rago.
    Tarungume littafin tashiga barci.

Dak'ar ta iya tashi da asuba tayi sallah, shed'an yaribace ta ta hau barci, wannan yasata makara gashi tanada lecture d'in safe, agurguje ta shirya tanufi aji.
    Duk da haka saida ta makaro domin kuwa uncle G! Yarigata shiga, taja tunga ak'ofar class d'in, inda sauran d'alibai makararru suke irinta.
    Tsaye yake yana gabatar da lecture, jikinsa sanye da blue d'in shadda d'inkin boda, bawata mai tsada bace, amma yayi k'yau, domin dama mai k'yawunne, babu abinda kakeji sai k'amshin turarensa, jiyay hancinsa yana shak'o masa kamshinta, yad'an juyo inda yake zatonta, kallon ido cikin ido sukayima juna, dukda idanunsa suna cikin gilas wannan bai hanata jin wani yarrrrrr! Ba, tai saurin kauda kai daga kallonsa, ya gyara tsayuwarsa yana wani d'an murmushin mugunta, yacigaba da gabatar da darasi.
     Su sopy suna tsaye tareda suran maka rarrun d'alibai, har yagama lecture yafito, kallo d'aya sopy tai masa ta kauda kai, shikuma yawuce yana murmushin mugunta, wanda yabama sauran d'aliban mamaki, wasu kuma yabasu haushi dan aganinsu ya raina musu hankali, tunda akwai sa'aninsa agurin.

Ya k'arasa office d'insa amma saiyayi turus ak'ofa domin ganin kairat zaune, ya had'e rai ya ce, "lafiya dai??
    Kairat tad'ago tana kallonsa, lafiyarce takawo hakan.
   Yakuma tamke fuska ya ce, "miya kawoki office d'ina nace??.
    Yanda yayi maganar cikin tsawa saita tsorata, dan tasan baya son wargi, cikin rawar murya ta ce, "dama nazo nasanar dakai dadyna zai maidani karatu AMERICA.
    Uncle G! Ya tab'e baki, lallai yayi dabara, to ALLAH ya taimaka, zaki iya tafiya.
   Kairat ta kalleshi cikin matuk'ar bak'in ciki, dan ganin yanda yake korarta, ta daure ta ce, "to ya maganarmu dan inaso nasan matsayina agurinka!!.
    Saida yay mata kallon sama da k'asa sannan ya ce, "bakida wani matsayi agurina kamar yanda nasanar dake, sai dai ina miki fatan alkairi a rayuwarki",     ya nuna mata k'ofa akaro na biyu, zaki iya tafiya dan inada abinyi.
     Wani bak'in cikine ya tokare mak'oshin kairat, tai waje cikin bak'in ciki, dan idan tayi magana kuka zai iya zuwa mata.
    Uncle G! Yaja tsaki, yana fad'in 'yar wahala, indai so nane kin d'akko abinda yafi k'arfinki, domin tuni wata ta karb'e zuciya ta,  useless! Kawai.

Kairat d'iyar wani mai kud'ice, tunda aka kawota makarantar nana ta k'yalla ido akan uncle G! Taji takamu da sonsa mai tsanani, sai dai shid'in batai masaba, yafison ya auri d'iyar talakawa irinsa.....................✍🏻






💞bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 25~October~2016



🔷 🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM 💞




🔶🔸2⃣5⃣🔸🔶

............Safiyya! kam tunda uncle G! Yafita tashiga aji tazauna zuciyarta cike da tunani iri iri, koda zaliha! ta zauna kusada ita tana mata surutun data saba bata kulataba, saima ta d'akko wayarta tana catin da uncle kabeer.
    Wani sak'o yashigo amma saitayi burus dashi, dan azatonta wanine ya d'auki nomber d'inta a group dan haka wasu keyi, musamman ma samari.
     Shigowar wani malami yasa ta daina catin d'in, tanatsu domin d'aukar lecture.
   Bayan fitarsa batada wata lecture sai k'arfe uku, dan haka tanufi library domin wani bincike.
    Ta shak'i wani k'amshi wanda tabbas tasan mai shi, amma saita share tacigaba da karatunta, jin k'amshin ya yawaita agurin yasata juyowa domin tabbatar da zarginta.
    Uncle G! Ne tsaye yana binciken wasu books saidai da alama bai gantaba, dan haka tak'ara k'asa da kai, bata buk'atar yaganta.
   sai dai ta makaro, domin kuwa tunda ya shigo da ita yafara tozali, ya basar ne kawai yanuna bai gantaba.
    Cikin takunsa na masu aji da gayu yanufo inda take zaune, hannu biyu yasa yadafe tebir d'in gabanta, tareda fad'in Assalamu alaiki?.
   Da sauri tad'ago dan batai tsammanin zuwansa ba.
  Ya ce, "bakijin sallama ??.
Cikin rawar murya ta amsa, ta d'ora da gaisheshi.
   Yaja kujera ya zauna yana fad'in ya ykk?
  Sopy taja numfashi tana fad'in lfy law.
  Ya ce, "good".
Kafin yayi magana wayarsa ta hau k'ara alamun kira, ya cirota daga aljihun gaban rigarsa ya amsa.
  Saida yagama wayarsa sannan yadawo da dubansa gareta, yayinda wasu d'alibai dake library d'in suke kallonsu.
   Ya mik'e yana fad'in kisameni a office inaso muyi wata magana dake, domin inaso naje gida wannan week d'in akan maganar aurenmu!!.
   Da sauri ta kalleshi, shima kallonta yakeyi, dan haka ta maida kanta k'asa, ya kwashi wasu takardunta data ajiye, ta daure ta ce, "uncle zanshiga lecture dasune fa.
   Yatafi yana fad'in nasani idan kinzo saiki karb'a ina jiranki karki b'ata min lokaci.
   Sopy ta dafe kai tana fad'in nashiga uku ni safiyya mutumin nan fa yafara shiga min hanci, yakamata na face shi, kanta ta maida ga karatu amma saita kasa karatun dole ta mik'e tafice, tadad'e tana tunanin zuwa office d'insa, dan gsky bataso azargeta akan yawan shiga office d'insa.
   Wayarta ta hau wringing, tad'aga tana mita.  
  Muryar uncle G! Taji yana fad'in ina jiranki fa!!.
  Kafin ta ce, "wani abu ya yanke wayar, ta dafe kai tana fad'in ya salam, dole ta daure ta nufi office d'in.
   Ta kwankwasa, ya ce, "shigo mana, dan yasan ita ce!!.
  Da sallama tashiga kanta ak'asa, yad'ago yana kallonta batareda ya ce komaiba.
  Jin yayi shiru, ta ce, "gani!!."
Ya ce, "aii naganki, ya maida kansa kan abinda yakeyi.
  Sopy tabishi da kallo cikin takaici, takardunta yake dubawa, taja k'aramin tsaki amma baiji ba, a zuciyarta ta ce, "kaidai kana son sakani cikin matsala, banason wani yazargeni wlhy.
   Ya d'ago yana fad'in wai bazaki zaunaba ne??.
   Ta ce, "nanma ya isa.
Ya ce, "okey nima bari nataso tunda yau tsayuwar kike sha'awa.
   Kafin ta ce wani abu yataso, ya k'araso inda take tsaye, jingina yayi ajikin bango ya hard'e hannayen sa a k'irji, ya dasa mata fararen idanunsa manya masu yalwar gashi.
   Ta k'ara k'asa da kanta dan ganin irin kallon k'urullar dayake mata, ya murmusa dan ganin yanda taketa sinne kai kamar wadda tayi k'arya, ya gyara tsayuwarsa, sopy!! Wai sai yaushe zaki kalli cikin idanuna ne, kunyarki tayi yawa fa.
   Hannu tasa ta rufe fuskarta.
 Yay dariya tareda fad'in okey to shikenan, dama inason nasar dake jiya da daddare naje gidanku!!.
    Ta zaro idanu, gidanmu kuma??
  Ya jin jina kai, e, gidanku, aii dama na ce, "miki bada wasa nazoba, yacigaba da fad'in, munyi magana da baba, nasar dashi komai nida kabeer, yakuma karb'eni fiye da zatona, yanzu haka yabani izinin turo iyayena! Sai dai ya ce, "bikinmu zaikai nanda watanni dan yanzu suna shirin bikin kabeer, amma bayan bikin kabeer da wata uku zuwa hud'u sai ayi namu.
    Sopy ta zame ta zauna a k'asa, bayanta jingine da k'ofa.
  Ya bita da kallon mamaki, ya daure ya ce, "yaya dai? Ko hakan bai mikibane??.
  Ta d'an kalleshi, ta girgiza kai.
Ya ce, "to miye matsalarki??.
Ta ce, "babu, ta cigaba da fad'in nasan iyayena bazasu cutar daniba, dan haka na amince da duk abinda suka yanke, kuma zan yimusu biyayya.
   Uncle G! Yaja ajiyar zuciya yana fad'in ALHAMDULILLAH!!, ya tsugnna a gabanta, ya ce, "karki damu safiyya!, kabeer ya sanar dani abinda yafaru dake a baya, tsakaninki da AMINIYARKI da kuma SAURAYINKI, to inaso ki manta da abunda yafaru a baya, ki gogeshi a arayuwarki, kid'auka yanzu zaki sake sabuwar rayuwane, ki yarda ni ne!! Zab'in alkairin da ALLAH yay miki, zan baki mamaki insha ALLAHU, Zan rik'e amanar da baba yabani taki kinji.
   Yaja numfashi, gobe idan ALLAH yakaimu kabeer zaizo, zai sanar dake sauran bayani, ni kuma jibi idan ALLAH ya kaimu zanje nasanar da iyayena, ya mik'a mata farin hankici daketa tashin k'amshi, karb'i ki goge hawayenki dan banason su zuba k'asa.
   Sopy ta karb'a dan ita bama tasan tana kukaba, saidai batasan kukan na miyeba?? Farinciki ko bak'incikin rabuwa da Abdul, tasan tabbas uncle G! Yafi Abdul komai kyau, ilimi, aji, da sauran abubuwa masu yawan gske, kud'i kawai mahaifin Abdul zai nunawa uncle G!, itakam bata d'auki kud'i wani abu mai muhimmanciba arayuwarta, dan itama talakace tib'is, tanada tabbacin samun nutsuwa a gidan talaka d'an uwanta.
   Jitai uncle G! Yana fad'in to kukan ya isa haka, inko bahakaba zan lashe hawayen dasuka sake zubowa.
  Hannu tasa tasa tarufe fuska tana dariya.
  Shima dariyar yayi, "wai yau miyasaki makara ne??
  Cikin sanyin murya ta ce, "karatun tarihinka mana.
Ya ce, "nice, hakan yayi nasan yanzu kinsan ni kowaye, ni talakane tib'is, sai dai rufin asirin ALLAH kawai, ina fata wannan bazai shafi auren muba ko??, Dan kinji wayeni dakuma inda nafito,  kinji su waye family nawa, zaki iya neman k'arin bayani a wajen kabeer, dan yasan komai a kaina. 
   Tai murmushi to aii nima talakace, nasan kuma kasani, tunda kana tareda uncle kabeer.
  Yad'an murmusa yana fad'in to shikenan ALLAH ya tabbatar mana da alkairi, amma daga yau idan kika k'ara makara a lecture d'ina tofa bayan horon hana shiga aji, akwai horo tsakanina dake, dan haka ki kiyaye, yafad'a yana mik'ewa.
   Itama ta tashi tsaye, to bari na tafi.
  Kai habadai tun yanzu, nifa ban gaji da ganinkiba!!.
   Hannu tasa ta rufe fuska ta ce, "aii munkusa shiga lecture ne.
Yay dariya to sarkin kunya, ga kayanki can jeki d'auka.
   Ahankali ta nufi tebir d'in sa, ta tattara takardunta ta kwaso zata juyo wayarsa ta hau wringing, ya ce, "taho min da phone d'ina!.
   Saida ta d'an rissina sannan tabashi tay waje da sauri,  dan batason yasake tsayar da ita.
   Yay murmushi, yana binta da kallo...............[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 26~October~2016



🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💞




🔶🔸2⃣6⃣🔸🔶

...........Tunda tabar office d'in tazama wata shiru shiru, gaba d'aya abin mamaki yake bata jitake tamkar amafarki, wai itace zata zama matar uncle G!, kai wannan lamari tamkar ba gsk bane, lallai ko bata son uncle G! tofa dolene ta aureshi, kodan ta k'ara nisanta kanta da Abdul, da fareeda, wasu hawaye suka zubo akan kumatunta, wlhy tana son fareeda, amma gashi fareeda tajawo abinda yanisantasu da juna, tana matuk'ar kewarta da son ganinta, takifa kanta saman tebir tana kuka.
   Zaliha ta tab'ata, sopy lfy dai ko? Sopy tad'ago tana kallon zaliha, fuska share share da hawaye, ta ce, "babu komai wlhy zazzab'i nakeji".
   Ayya sannu to kitashi na kaiki hostel mana.
  Sopy ta girgiza kai ki bari mu gama lecture tunda saura d'aya.
  Zaliha ta ce, "to shikenan", amma fa wata magana najiyo yanzu akanki!!.
    Sopy ta ce, "akaina kuma zaliha??, wace irin magana kenan?.
   Zaliha sarkin gulma ta gyara zama, wlhy wasu samari naji suna fad'in way soyayya kukeyi keda uncle G! Wai shiyyasa kikema samari girman kai, dan anga wai yabiki library d'azu.
    Sopy ta k'urama zaliha idanu, kamar zata cinyeta, saida zaliha ta tatab'ata, sannan taja ajiyar zuciya, zaliha ta ce, "mi kuma kike tunani?
   Sopy ta girgiza kai babu komai, amma ni k'arya suke min, dan kawai sunga yashiga library sai suce wajena yaje.
   To aii wai bayan fitowarsa ke kuma kinje office d'insa!.
   Sopy taja tsaki, ta ce, "kai magulmaci madai yaji haushi wlhy, to uncle G! Abokin uncle d'inanane tare sukai karatu a wannan makarantar, wannan itace dangan takar dake tsakaninmu, sai a daina gulmarmu aii, ta maida kanta ta kwanta.
    Zaliha uwar gulma aka jinjina kai, kinsan ba kowane yasan hakaba, dan nima dabaki fad'aba ban saniba, dan wlhy nima nazata soyayya kukeyi, to ammafa kallon dayake miki irin na masoyane, idan fa yana lecture to gaba d'aya hankalinsa yana kanki, to kinga aii masu fad'a basuda laifi.
   Banza sopy tayi mata, dan tasan zaliha magul maciyace tafad'a aji, ita ba k'ok'ariba sai iyayi da gwalli.
   Ganin sopy ta shareta sai tatashi ta fita, wajen samarin ta nufa tazauna, suka shiga tambayarta zaliha tagaya miki, zaliha ta rik'e baki tana fad'in kukam magulmatane wlhy, idan ance maxa sun iya gulma ku musa mana, to ta ce, "wai abokin uncle d'intane.
    Wani acikin samarin ya ce, "kai wlhy ban yardaba, k'arya ta fad'a miki, amma kicigaba da saka mata ido zaki hano gskyr maganar, zaliha tamik'e tana fad'in aiko saina gano bari naje dan za'ayi mana lecture yanzu.
   Samarin suka shek'e da dariya, suna fad'i zaliha dama ke kina fahimtar karatune.
   Zaliha ta hararesu tai gaba, dan tasan magana suka gaya mata.

Koda sopy ta koma d"aki takasa aywatar da komai, tunani ya bai baye kwakwalwarta, ji tai yau son Abdul ya dawo mata sabo azuciya, jitai a yau zata iya auren Abdul suyi kishi da fareeda, ta rintse ido ta bud'e tana fad'in, ya ALLAH idan shaid'an ne yake k'awata mini hakan ALLAH ka dawo dani cikin hayyacina!, ta fashe da kuka tana girgiza kai, wlhy bazan iya zaman kishi NI DA AMINIYATA ba har abada, fareeda na hak'ura na bar miki Abdul har abada wlhy, nabar miki! Na bar miki!!! Ta k'arasa fad'a cikin kuka mai ban tausayi, masu karatu nimadai saida na matse hawaye dan sopy tabani tausayi.
    Ta dad'e tana kuka daga k'arshe ta dangana, tayi shiru, sai shashsheka da takeyi, dahaka wani waha lallen barci ya d'auketa.
   Da safe da ciwon kai mai tsanani ta tashi, dan haka bayan gama sallar asuba saita koma barci.
     Wringing d'in wayartane ya tasheta, sunan uncle kabeer tagani akan wayar, ta tashi da sauri, tana amsa wayar, bansan miya fad'a mataba ta tashi da sauri tahau shirin fita.
   Kai tsaye office d'in uncle G! Tanufa dan tasan uncle kabeer yanacan, ta kwankwasa aka bata izinin shiga, da sallama tashiga, suka amsa mata,  ta rissina tana gaishesu.
    Uncle kabeer ya d'ora da fad'in my daughter ya dai? Naganki kamar kina cikin damuwa?,
   Sopy ta girgiza kai, ta ce, "uncle lafiyata k'alaw kainane kawai keyin ciwo.
   Ayya sorry my daughter, yanuna mata kujera ta zauna, uncle G! Ya ce, "kinsha magani ko?.
   Ta ce, "e nasha shine ma yasakani barci.
Okey ALLAH yabaki lfy.
  "suka amsa da amin."
Uncle G! Yamik'e yana fad'in bari naje nagabatar da lecture.
  Okey lecturer!! Uncle kabeer yafad'a cikin tsokana.
  Uncle G! Yafita yana fad'in kana nan baka canjaba kabeer.

Bayan fitar uncle G!, uncle kabeer yadawo da hankalinsa ga safiyya da kanta yake kasa tana wasa da zoben hannunta yay gyaran murya, sopy ta d'ago tana kallon sa, yay mata murmushi d'iyata yaya dai??.
  Itama ta murmusa ta ce, "bakomai uncle.
   Ya ce, "okey to shikenan, dama wata magana ce takawoni, duk da youseef yasanar dani kun fara maganar jiya ko??.
   "E, uncle! Hakane".
Uncle kabeer ya ce, "to ke yakika gani?? Kin amince??.
   Sopy tay kasa da kai saboda kunya.
   Karki damu d'iyata, karki bari kunya tahanaki fad'ar gskyar ki, inhar baki sonsa ki sanar dani.
   Sopy ta rufe fuska da hannuta ta ce, "ina sonsa uncle!!.
   Uncle kabeer yay dariya, "ALHAMDULILLAH", yafad'a yana gyara zama, lallai ina tayaki murna d'iyata!!, da samun miji nagari mai addini da tarin ilimi, nasan watarana zakiyi alfaharin kasancewar youseef a matsayin mijinki, zakiji dad'in zama dashi domin kuwa mutumin kirkine shi, ALLAH ya kaimu lokacin musha biki.
   Sopy taja hijjab  ta rufe fuska.
  Uncle kabeer yayi dariya, bazakice amin ba sopy.
   Ta ce, "kai uncle wlhy kana bani kunya.
 To bani kunyata uncle kabeer yafad'a.
   Haka sukaita hirarsu, har uncle G! Yadawo, tunda ya shigo bakin sopy ya mutu, ta daina magana takuma sunkuyar da kai k'asa.
    Uncle G! Ya nunawa uncle kabeer sopy da baki, uncle kabeer yay dariya ya ce, babu ruwana nidai, kunfi kusa.
   Sopy ta d'ago karaf ta kama uncle G! Yana mata gwalo.
  Batasan sanda ta harareshiba, ya ce, niko!!. 
 Saida taje bakin k'ofa sannan ta ce, "e, ta fita da gudu.
   Dariya sosai sukeyi, uncle G! Ya ce, "kabeer dama haka safiyya take??.
   Uncle G! Yay dariya ya ce, bazakaji mutuwar sarki abakinaba.

Haka rayuwa tacigaba da tafiya, sopy tana karatu yanda yakamata, takanje gida weekend lokaci2 idan tasamu dama, shak'uwa kuma tana k'ara shiga tsakaninta da uncle G!................✍🏻 




💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 27~October~2016




🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA  BILKISA IBRAHIM 💞




🔶🔸2⃣7⃣🔸🔶

..........BARI MU WAYWAYI FAREEDA....
   Fareeda kam rayuwa ta canja mata, kwance take tana fidda numfashi da k'ar sakamakon zazzab'in dake jikinta, babu abinda ya haddasa mata zazzab'in sai uban aiki da umman Abdul tasakata, dak'yar tagama aikin tajawo jiki tazo ta kwanta.
   Abdul yashigo ko sallama babu, ko kallo bata isheshiba ya wuce yana canja kaya, fareeda tabishi da kallo tana zubar da hawaye.
   Ya gama yanufi hanyar k'ofa domin fita, ta daure ta ce, "Abdul!!.
   Ya juyo yana kallonta awulak'ance batareda yayi maganaba,
   Cikin kuka ta ce, "dan ALLAH Abdul inaso muyi magana, ka taimaka kazauna.
  Ya gyara tsayuwa kinga malama idan zaki fad'a ki fad'a dan babu wani zama dazanyi, inada gurin zuwa.
   Fareeda ta cije baki, cikin k'arfin hali ta tashi zaune.
  Ta ce, "Abdul dan ALLAH miyasa ka juya mini baya, yakamata ka fahimceni, yanzu ka daina kula dani, kana ganin wahalhalu dana ke ciki agidannan ga gallazawar mahai fiyarka amma baka tab'a nuna rashin jin dad'in kaba, dan ALLAH karka barni Abdul, yanzune nafi buk'atar zama dakai Abdul, karka manta saboda kai nabar iyayena, nabar 'yan uwana, nabar aminiyata mai sona dason ganin farincikina, amma danmi zaka barni bayan yanzu kai kad'ai gareni, saikuma wannan cikin dakake gani bai dace yazoba ayanzun.
   Abdul yaja tsaki, yanuna ta da d'anyatsa yana fad'in, wlhy idan kina tare da wannan shegen cikin bazaki tab'a samunaba, zaki cigaba da rasa abubuwa arayuwarki kuwa, kamar yanda wad'ancan mutanan suka barki to nima haka zan barki, amma har yanzu kinada sauran dama, inhar kika yarda aka zubar da wannan cikin tofa zan dawo miki a matsayin Abdul d'inki nada, inko har kika cigaba da bijirewa buk'ata ta tofa zaki shiga k'angin rayuwa wanda yafi na yanzu, kuma bazaki raini d'an dake cikinkiba agidannan, dan nafad'a miki ban shirya haihuwaba yanzu, ban shirya zama uba ba yanzu, amma kikayi sakakin d'aukar ciki saikace wata akuya, acikin wata biyu da zuwanki, ke wlhy yanzuma dan abbana ya hanani sakinkine, amma kicigaba da zama akan taurin kanki kigani, idan ban yi waje dakeba, nabaki nanda sati biyu ki yanke wadda zata fisheki, ko ki yarda azubar da ciki, kicigaba da zama dani, ko kik'i yarda nayi waje dake.
   Fareeda ta fasheda kuka ta ce, "haba Abdul kayimin adalci mana cikinnan fa d'an kane, ta hanyar aure muka sameshi, kuma namiji shike bada kwan haihuwa, miyasa bazaka gane ba laifina bane? Kuma wlhy ana mutuwa wajen zubar da ciki ko mutum yarasa mahaifarsa, baka gudun d'aya acikin wad'annan yafaru dani ne??.
   Abdul yaja tsaki, yafice yana fad'in matsalarkice kuma wannan, nidai nafad'a miki buk'a tata, idan kin kiyaye kin tsira, idan kin cigaba da bijirewa zaki koma gidan tsohone.
    Kuka sosai fareeda takeyi dan duk taji kalaman Abdul na k'arshe, ta tura kanta cikin filo tana gunjin kuka, yaune rana ta farko data tab'ajin wani abu mai kama da nadama ya ziyarci zuciyarta, saidai har yanzu tana son Abdul d'inta, tanaji kuma a zuciyarta tafi safiyya sonsa walhy, lallai dolene tabi hanyoyin dazata magance matsalar dake tsakanin ta da Abdul, koda kuwa zubar da cinne, tunda shine tushen faruwar matsalarsu,😳😳 lallai fareeda bakida hankali.

Agidansu sopy kuwa anata shirin bikin uncle kabeer, sopy duk tazama busy sakamakon duk abinda uncle kabeer zaiyi saida ita, ga makaranta damma cikin weekend za ayi bikin, batada wani lokacin kanta, yauma suna gama lecture uncle kabeer yakirata akan tashirya gashinan zuwa zai d'auketa suje wani waje, gudu2 tayi wanka bata tsaya yin wata kwlliyaba ta zura doguwar riga ta shadda tasaka hijjab sai dai yau iyakarsa guywa tad'ansaka turare ta fito.
    Bata dad'e da fitowaba shikuma ya shigo cikin makarantar, bayan sun gaisa ta ce, "to uncle mutafi ko?.
   Ya ce, "sai mun jira youseef dan hardashi zamuje.
   Sopy tai saurin kallon uncle kabeer, uncle dammi sai da shi zamu?.
   Uncle kabeer ya ce, "dan yanada muhimmanci atafiyar.
   Sopy tayi shiru dan ita kam gsky bata son tafiya tare da shi, inhar yana guri bata sakewa, saboda tsananin kunyarsa datakeji......, muryarsa ce ta katse mata tunaninta, yak'araso yana fad'in sorry na b'ata muku lokaci ko?.
    Uncle kabeer ya ce, "A'a, itama aii yanzu tazo.
   Sopy ta daure ta ce, "ina yini sir! ?.
   Ya ce, "lafya lau maa!.
Uncle kabeer ya tuntsure da dariya ya ce, "one  one, kenan.
   Suka shiga mota suna dariya banda sopy datad'an murmusa kawai, tunda suka shiga mota sopy tayi tsit, sai dai duk d'agowar dazatayi saitaga uncle G! Ita yake kallo ta madubin gaba, ganin yasaka mata ido saita daina d'agowa ma gaba d'aya.
   Kasuwa sukaje, suka lodo kaya, na duk amfanin dazasuyi awajen biki, tundaga kayan abinci da drinks, da duk wani abunda zasu iya bukata, sun siyo dai dai k'arfinsu, suka zubo amota suka kai inda zasu ajiye.
   Uncle kabeer ya ce, "auta saura d'inkinki ko?.
   Sopy ta ce, "uncle aii telan ya ce, "sai gobe idan ALLAH yakaimu.
   Okey to ALLAH yakaimu goben, yanzu bari mu kaiki makaranta ko?.
   Ta ce, "dan ALLAH uncle ka kaini gida gobe sai nadawo.
   Uncke G! ya harareta, saboda son yawo ko?? To makaranta zamu maida ke, dan goben da safe nine zan fara yi muku lecture, kuma harda test mai zafi, kinsan kuwa idan bak'ya nan hukuncin ki yafi nakowa.
   Uncle kabeer ya juyo yana kallonta, to kinji fa, kinyarda na kaiki gidan??.
   Sopy ta d'ago ta kalli uncle G!, daya tsura mata fararen ida nunsa masu haske, tai saurin maida kanta k'asa kamar xatai kuka.
  Uncle kabeer ya ce, "sopy shagwab'arki tayi yawafa, ko kin manta kin girma, nafa kusa aurar dake.
   Aii kamar jira take saita rushe da kuka.
   Sukuma sai dariya ta kufce musu, suka fita daga motar suna dariya, uncle G! ya ce, "gsky kabeer bakada kirki, ya bud'e baya yashiga inda sopy take zaune, yakai hannu zai kama hannunta saita k'ank'ame jikinta, shima saiya fasa,.
   Cikin taushin murya ya ce, "to kukan ya isa haka, ke dai abu kad'an sai kuka, kabeer ya shagwab'aki dayawa.
   Ta turo baki gaba, ya ce, "hummm, ashe idan baki maida bakin nanba zan tsotseshi yanzunnan.
   da sauri ta rufe fuskarta, ta kama k'ofa zata gudu, amma sai tajita gam arufe.
   Ya murmusa da ina zakije??
Ta ce nidai kutafi na fasa zuwa gidan.
   Uncke G! Ya ce, "aii dama dole ki fasa, tunda na hana, ya mik'a mata wata leda ga wanna kiyi kwalliyar biki ko,.
 Ta ce, "uncle kabeer da babafa duk sunyimini d'inki.
  Ya ce, "to aii nasu daban, nawa daban, su iyayene, nikuma mijine.
  Tai k'asa dakai tana fad'in nagode ALLAH yak'ara bud'i.
   Ya murmusa dan jin dad'in addu'arta gareshi, yad'ora da fad'in, kamar yanda nayi miki alk'awari gobe zan aika a d'akko miki Aysha.
   Da sauri ta ce, "dan ALLAH dagaske sir!.
   Uncle G! Ya harareta oh, bazaki daina cemin sir! D'innan ba ko?.
   Ta ce, "to aii dai sunankane ko.
 Ya ce, "humyim, zanyi maganin bakinki, nan bada dad'ewaba.
  "Shiru tayi masa."
Yayinda uncle kabeer yashigo motar yana fad'in kunga kumuje nifa inada aikin yi, dannaga ku soyayyace agabanku.
   Sopy ta ce, "kai uncle nidai dan ALLAH kabari.
   Uncle G! Ya koma gaba yana fad'in kaidai anyi uban banza, nikam ban more sirikiba.
   Uncle kabeer yay dariya yace, "habawa kaidai kabini ahankali idan ba hakaba na hanaka d'iyar.
   Taf, dakasha matsa kuwa, kaga aii kabayar da wuriko?? uncle G! Yafad'a yana tada motar...................✍🏻




💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 28~October~2016



🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💞




🔶🔸2⃣8⃣🔸🔶

...........biki dai ya kankama, komai yana tafiya yanda akeso, Aysha k'anwar uncle G! Tazo, sopy tayi farincikin ganinta, itamadai Ayshar! sopy! ta burgeta, tana ganin kuma ida yayansu ya aureta bazasu samu matsalaba, dan suma talakawa ne kamarsu, kuma gidan mutunci.
   Duk inda sopy tashiga Aysha na biye da ita, wannan yasa tasamu sauk'in wasu ayyukan, uncle G! Kam bata ganinsa domin suma suna can suna hidimominsu.
  
Yau aka d'aura auren KABEER MUKTHAR da ASIYA ALIYU d'aurin auren yasamu halartar mutane masu yawa, musamman abokan aikinsa da kuma wad'anda sukayi karatu tare, ga mutanen baba suma, to saimuce ALLAH yasanya alkairi uncle kabeer ALLAH yabada zuri'a d'ayyiba, nanda wata tara mu dawo suna.
    Da daddare aka kai amarya d'akin mijinta, su sopy sun isa gidan tun kafin zuwan amarya, amarya da danginta suka iso, anyi musu tarba ta mutunci, bayan an kammala abubuwan al'ada, motoci suka kwashi mutane domin maidasu gidajensu, amma sopy da Aysha sunanan, uncle kabeer ya ce, "su tsaya su gyarama amrya inda aka b'ata, dan k'awayenta sun tafi dan gudun karsu rasa motar dazata maidasu gida, bayan tafiyar kowa suka k'uk'e suka gyara gidan suka bajeshi da k'amshi, wajan k'arfe tara abokan ango suka rako angon k'amshi.
   Sudai su safiyya k'ofar gida suka koma domin jiran su, basufi minti talatinba suka fito, motar uncle G! Suka shiga ya maidasu gida, a k'ofar gidansu sopy uncle G! ya ce, "Aysha tashiga gida, Sopy ta ce, "to nima aii gidan zanje.
  Ya ce, "A'a zamuyi magana ne.
Dole tayi shiru.
   Bayan fitar Aysha, uncle G! Ya kalli sopy, ita kuma tayi k'asa da kai, ya d'an murmusa yana fad'in Safiyya! sarkin kunya.
  Yanda yakira sunan nata saida tsigar jikinta ya tashi, tabbas babu wanda ya iya fad'ar sunanta kamar uncle G!, yakan fad'i sunan dawani irin yanayi mai saka mamallakiyar sunan cikin wani irin yanayi.
   Yay gyaran murya, tareda k'ara ambatar Safiyya!!
  Itama cikin sanyin muryarta mai zak'i ta ce, "Na'am.
  Yad'an gyara zamansa, ina ganin gobe idan ALLAH ya kaimu zan maida Aysha gida, daga nan kuma zan taho da magabatana domin kawo kud'in aurnmu!!.
  Sopy tayi shiru tana tunani, yad'an buga yatsunsa biyu sukai k'ara, ta juyo tana kallonsa, yay murmushi tunanin mikikeyi ne?.
 Ta ce, "bakomai, amma dan ALLAH kabar Aysha tad'an k'ara kwana biyu.
  Ya ce, "bazai yuwuba Safiyya saboda Aysha tana makaranta kuma kinga gobe litinin, tamayi asarar karatun goben kenan.
  Sopy ta ce, "hakane, amma dan ALLAH idan anyi musu hutu zaka kawota.
  Karki damu, zatazo insha ALLAHU sannan ma kina gidanki!.
   Tasa hannu tarufe fuska.
Humm sarkin kunya kenan, nikam kar kunyarnan ta cutar dani a abayan aure.
  Bata ce, "komaiba tabud'e motar ta fita.
 Yay murmushi to saida safe tunda babu sallama.

Washe gari uncle G! Yazo d'aukar Aysha, da kuka suka rabu da sopy, inna tanata lallashin Aysha, haba Aysha kukan ya isa haka mana, insha ALLAHU kwanannan ma zata dawo wajenku kinji, kiyi hak'uri kibar kuka ya isa haka.
  Da haka dai sopy tarako Aysha wajen uncle G! Dake k'ofar gida, yabisu da kallon mamakin dan ganin idanunsu duk hawaye, ya jinjina kai yana fad'in sannunku da kuka, saikace wad'anda zasu mutu.
   Sopy ta gaidashi ya amsa yana kumshe dariya.
   Ahaka dai sukai sallama, uncle G! Yaja mota suka tafi, tunda suka tafi Aysha take kuka, saida uncle G! Yadaka mata tsawa sannan tayi shiru.
  Cikin fad'a ya ce, "kinbi kin dameni da kuka, saikace har abada bazaku sake had'uwa ba? Inhar bakimin shiruba to wlhy zan tsaya na zaneki anan.
  Tasan halinsa sarai dan haka tayi shiru, ta ce, "yaya dan ALLAH kayi hak'uri wlhy aunty safiyya tanada kirki, duk wanda ya zauna da'ita dole yayi bak'in cikin rabuwa da'ita, dan ALLAH yaya kuyi aure da wuri dan tadawo gidanmu gaba d'aya.
   Uncle G! Yay murmushi oh Aysha kinda abin dariya wlhy, to wai mi auntyn nan taki tayi miki hakane kiketa yabonta??
   ALLAH yaya sunada yawa, yanzu haka bakaga tsarabar datayo minba, ta gwaggo da ban ta baba daban hardasu aunty hafsat ma duk tayi musu suma.
   Uncle G! Ya jinjina kai lalai aunty tana jidaku, kenan ni kad'aine batayima tsarabarba??. Aysha tayi dariya to yaya ai kai kuna tare kulum shiyyasa.
   A'a bawani muna tare ita dai ta wareni kawai.
   Haka sukaita hira har zuwa gida.

Itamadai sopy tunda suka tafi taiyi shiru dan tana k'aunar Aysha, yarinyar tanada shiga rai ga wayo da son aiki, zuwan su aunty NAFISA ne yasaka tad'an ware, suka shiga aikin gyaran gida, da kaiwa mak'ota kwanikansu da sauran abinda aka aro domin yin amfani, dayake duk danginsu anan cikin kano suke, sai yazama babu kowa a gidan sai isu isu, inna dakanta ta shirya karin kumallo sopy taje takaiwa su uncle kabeer.....................✍🏻





💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 29~October~2016


🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💞




🔶🔸2⃣9⃣🔸🔶

........Gwaggo ta tari autarta da murna, dan kwana biyunnan tayi kewarta, Aysha ta ce,"gwaggo wlhy nayi kewarki kwana biyu, sai dai naji dad'in zuwa kano.
   Gwaggo ta ce, "kai auta fad'i gaskiya dai, kinga yanda kikai haske da k'iba a kwana biyunnan kuwa, mikike cine haka? .
   Aysha tayi dariya, aii wlhy gwaggo bazasu lissafuba, kai matar da yaya zai aura tanada kirki gwaggo gata mai k'yau.......tayi shiru domin shigowar uncle G!.
   Ya ce, "to uwar surutu ince har kin fara zubama gwaggo shi.
  Gwaggo ta ce, "to badoleba tayi kewanane aii.
  Uncle G! Yazauna a kan tabarmar dake shimfid'e ad'akin yashiga mik'a gaisuwa ga gwaggo.
   Gwaggo ta amsa cikin fara'a, ta ce, "ya aikin? Da abokan zama?.
   Wlhy lfy law gwaggo sunata gaisheku, da kuma godiya.
  Kai haba saikace wani abu, mu abinda kabiru yay mana aii bazamu iya biyansaba.
   Uncle G! Yay murmushi, ya ce, "gwaggo ina baba yake?.
    Baban ku yana wajen zana idar malam haruna mai gari.
   ALLAH sarki, gwaggo malam haruna yarasu?.
  Wlhy kuwa d'annan yanzu badad'ewa aka fad'i mutuwarsa, inagama ba'a binnesaba.
   To ALLAH yagafarta masa da dukkan musulmai baki d'aya, amma mutuminnan yasha wahalar jinya, ALLAH dai yasa kaffarane.
   To amin gwaggo tafad'a tana mik'ewa, bari nakawo muku ruwa, munata surutu ko ruwa ba'a bakuba.
   Uncle G! Ya ce, "bakomai gwaggo da kin barima Aysha saita d'ebo aii, gwaggo ta ce, bari nad'ebo tunda natashi, saima ahad'o da abinci, saidai kuma ban bayar ansiyo maka awarar taka ta famaba, wannan tararrabin rasuwar ya mantar dani,, Aysha taso ki siyo masa, ALLAH yasama bata k'areba kinsan Awarar uwaliya kamar nama take agarinnan.
  Aysha ta ce, "to gwaggo kawo kud'in??, ki d'akko a k'ark'ashin filo, akwai d'ari biyu.
  Uncle G! Ya ce, "karb'i barmata kud'inta, ya mik'a mata dubu d'aya, ta ce, "yaya daka bari na d'auki d'ari biyun dan wlhy sai kaga anata neman canji ak'isamu.
 Ya ce, "to, kuma kiyi sauri, dan karki zauna neman zance.
  Aysha tafita tana turo baki.
Gwaggo tashigo da ruwa a kofin silba, ta koma ta d'akko samira ta ajiye gaban uncle G!, ya ce, "yawwa gwggonmu sannunki da aiki.
   Ta zauna tana fad'in aii kune da sannu, kuda kuka sha hanya, ya d'auki ruwan yasha, yana murmushi, suka cigaba da hira kafin Aysha tadawo.
  Badad'ewa Aysha tadawo, sukaci suka k'oshi yafita danyin sallah da ta'aziyyar rasuwar da'akayi.
     Baba yashigo, Aysha taje ta taroshi cikin farin ciki, A'a Ayshatu! saukar yaushe??, aysha tayi dariya baba tun d'azu mukazo harda yayama.
  Ya ce, "madallah ina yusufan yake?, baba yanzu yafita sallah baku had'uba?, A'a bamu had'uba, k'ila masallaci juma'a yaje sallar dan sune naji sun tada sallah yanzu.
  Saida yay gasuwar yadawo, ya tsugunna ya gaida baba, baba ya amsa cikin fara'a, yusufa! ya jama'ar birni?, dasu kabiru ango??.
  Wlhy lfy law baba, yanata godiyar d'awainiya.
   Kai haba in banda abin kabiru miye na godiya, abun nawa yake, tunda ALLAH bai nufa zamu d'aurin aurenba.
   Aii bakomai baba hakanma angode ALLAH yasaka da alkairi, Aysha aii ta wakilceku.
  Sun dad'e suna hira, anan nema uncle G! Yasanar da baba maganar tura manya gidansu safiyya, ckin jin kunya yake maganar.
  Baba yayi dariya aii ko yusufa nayi farinciki da wannan magana, wlhy dama zamannan naka ya isheni haka, mutane sai surutu sukeyi wai dan kayi boko kak'i yin aure, sun manta aure lokacine.
  Uncle G! Yay k'asa da kai yana fad'in gsky ne baba, amma kuyi hak'uri.
   A'a aii bakomai yusufa tunda gashi lokaci yazo, aii mu sadai muce ALLAH ya kaimu lokaci, yasa kuma ayi da ranmu.
   Akan leb'ensa ya ce, "amin.
Bayan sun gama tattaunawa yafita domin ganawa da matasan k'ungiyarsa kamar yanda yasaba, domin suma tuni sun hallara gurin dasuke had'uwa tunda sunsan da zuwansa.

Da dadadare aunty hafsat suka zo itada libabatu dan tuni Aysha taje gidajensu takai musu labarin matar da yaya zai aura, harda tsarabarsu, sannan ma shi bai dawoba yana waje.
   Basu dad'e da zuwaba ya shigo shima, ya ce, "A'a 'yan uwa kune da daddarennan??
   "Sukace mune!!.
  Yaja kujera 'yar tsugunno yazauna, suka gaisa, sukai masa godiyar tsaraba, ya ce, "wace tsaraba kuma aii ni! banyima kowa tsaraba ba.
   Aunty hafsat ta ce, "e, auta tace k'anwar muce tabamu ALLAH dai yasaka da alkairi yakuma kawo mana ita lfy.
  Uncke G! Ya ce, "to amin, yakuke da yaranku da mazajen!! ku?
  Suka ce, "duk muna nan lfy.
 Ya ce, "aii haka akeso.
Baba yashigo yana fad'in tofa yau gidan biki akene?
  Sukayi dariya, kowa ta gaidashi, sannan sukace munzo sannu da zuwane.
  Baba yazauna yana fad'in ince ko har Aysha taje muku?.
  Sukace aii baba tun d'azu ma kuwa.
  Ya ce, "auta kenan sarkin hidima, nan dai sukayita hira, harma baba yay musu bayanin maganar auren yayansu.
  Sunyi murna kwarai da gsk.

Washe gari uncle G! Yataho damasu kawo kud'in aure, anyi musu tarba ta mutunci, daganan komai ya gudana, atake kuma baba ya saka ranar aure nanda wata hud'u, iyayen uncle G! Sunji dad'i domin kuwa babu wani jan rai, bayan sun kammala uncle G! Yakaisu tasha suka hau mota domin komawa gida.

Haka rayuwa tacigaba da gudu da sauri, sopy tana karatu, kuma sukan yi hira jefi jefi da uncle G!, Dan bai cika takurata ba, saboda Baya son tasamu matsla a karatunta, yakan taimaka mata akan abinda yashige mata duhu, dukda har yanzu tananan cikin jin kunyarsa bata cika sakin jikintaba idan yana guru, zuwa wannan lokacin kuma labari yabaza makaranta cewa uncle G! Zai auri safiyya.
   Wasu har zuwa suke takanas domin ganin mai sa'ar data samu zuciyar tsadajjen namiji mai aji da ilimi irin uncle G!, dayawa sukanyi mamakin ganinta, dan azatonsu farace k'al kuma mai shegen k'yau👩🏻, wasu sukance dama masu k'yau basu cika zab'ar mace mai k'yauba, wasukuma sukanga safiyyan tadace da uncle G! D'in, domin itama tanada k'yau, sai dai k'yawunta mai b'oyuwane, irin wanda saika cika kallonta ko kana tareda ita kullum kake gani, to koma dai miye 'yammata saiku saurara domin kuwa safiyya itace tauraruwar uncle G!, dan shiyyasan sirrikan daya gano agareta.
  Magulmata dai anata aikin gulma, yayinda wasu 'yammatan suke jin haushinta dan sunnunama uncle G! D'in so amma yay burus dasu, itakam ko kallo basu ishetaba dan bata shiga sabgar kowa, garama Nadiya sukan d'anyi hira amma itama bakomai tasani dangane da sopy ba.
  Dan sopy ta daina k'awa bare AMINIYA, anriga anmata tabo azuciya akan AMINTAKA............✍🏻




💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YO[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 29~October~2016




🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷




NA BILKISA IBRAHIM💞




🔶🔸3⃣0⃣🔸🔶

........Akwana atashi babu wuya gurun "UBANGIJI", biki dai ya kankama, dukkan gidajen biyu sunata shiri, hakama uncle G! Yayi wuyar gani, ita kanta sopy baganinsa takeyiba, sai idan yaje musu lecture, ko kuma idan ya kirata a waya su gaisa.
  Yau da yamma Sopy tashigo anguwarsu, tana shigowa layinsu tayi kicib'is da Abdul, suduka gabansu ya fad'i, yabita da kallon k'urullah, itako ta tamke fuska kamar bata tab'a dariyaba, ta ratseshi zata wuce, da sauri yasha gabanta, takauce zuwa gefensa nanma ya tareta.
  Ta ce, "malam bani hanya nawuce.
   Ya ce, "haba gimbiyata ninefa Abdul d'inki mai sonki da k'aunarki, wlhy ina kewar rashin ganinki, dan ALLAH ki tsaya muyi magana.
   Ta balla masa harara tareda jan wani mugun tsaki ta ce, "kaga malam tunkafin na shuka maka rashin mutunci kabani hanya na wuce, wlhy Abdul natsaneka.
   Ya rinyse ido ya bud'e dan tabbas kalmar tata ta daki zuciyarsa, ya marairaice murya yana fad'in, Sopy nasan baki tsaneniba haryanzu kina sona, kina cikin b'acin ran abinda yafaru abayane, dan ALLAH kibani dama namiki bayani yanda zaki fahimceni, kece kad'ai nakeso kuma ashirye nake dana aureki ahalin yanzu.
   Sopy ta tuntsure da dariya, sannan ta tamke fuska tamkar ba ita tayi dariyarba, ta nunashi da d'anyatsa 👉🏻☹Abdul wai kaine! kake tunanin zama mijina!, tad'an murmusa, Abdul har abada bazan zama shashashar macen dazanyi miji irinkaba, ka d'auka SAFIYYA IBRAHIM KABEER ta sub'uce maka har gaba da abada, ta ciro kati daga jakarta ka karanta wannan shi kad'aima ya isa yabaka amsa, inama gayyatarka, dan nasamu miji mai tarin ilimi k'yau, aji mutunci, kai idan ina lissafa maka abinda ya dangan ceshi tofa sai mu kwana anan,kuma katashimin ahanya kafin natara maka mutane wlhy.
  Jiki asanyaye yamatsa mata ta wuce, tunda yafara karanta katin yake fitar da numfashi  mai kama da nishi, yajingina da bango gudun karya fad'i, cikin murya kamar mai kuka ya ce, "fareeda kin cuceni ALLAH ya isa tsakanina dake, kuma wlhy yau saikin gayawa aya zak'inta, yanufi gida kamar mayun wacin zaki.
  Da sauri muka bishi dan muganewa idanmu abinda zai faru.
      To bari mugani fareeda kota zubur da cikin??.
   Tunda nagabato b'angarenta nakejin ihun kukanta, wanda inada tabbacin suma mutanen dake gidan sunajinta, amma babu wanda yay yink'urin zuwa yaga abinda yafaru.
   Nak'arasa d'akin da sauri nida  madina, Abdul ne ke lakad'awa fareeda dukan 'yan danbe, duk yaji mata ciwo, amma wannan baisa ya daina d'irkartaba, dak'yar muka iya kwatarta, ya bimu da kallo yana huci kukuma daga ina??.
   Madina ta ce, "tofa, Abdul maida wuk'ar mu bak'in fareeda ne, yaja tsaki tozaku iya tafiya aii ko.
   Na ce, "kayi hak'uri Abdul kabari mu taimakawa fareeda kaga duk ciwone a jikinta, wata uwar harara yasakarmin, to aii ko uwar tace tazo gidannan saita fita, tunda sunce sun sallama mini ita, bareku gayyar sod'i, wlhy tun kafin nabud'e idanuna kubar gidannan idan kuwa bahakaba tokuwa jikinku  zai fad'a muku.
   Aii kafin yagama rufe baki madina uwar 'yan tsoro taja hannuna munyi waje, ta ce, "humm aunty bily naga mutuminnan yafara haukacewa wlhy zai iya dukanmu, kekam gaki lutiya idan yasamu wannan tsokar aii kinga takanki.
   Na balla mata harara ina fad'in ALLAH madi kin rainani, ni son k'ibar nan tawa nakeyi idan baki saniba.
  Amma gsky Abdul bashida mutunci irin wannan duka dayake mata kamar wata karuwarsa, kuma muta nen gidan sunaji amma sunk'i cetonta.
   Madina tayi dariya aii ni dad'i nakeji wlhy ALLAH yasa yay mata abinda yafi hakama, aii maganin maci amana kenan, kad'amma tagani.

To yaudai lefe ya iso na sopy, mota guda muta nen GURUM sukayo domin kawo lefen Safiyya.
   Akwati uku da karami na sama, babu laifi uncle G! yataka rawar gani, dan lefennan saidai mak'iyi amma yayi atalauce ba a sarauceba, anyi musu tarba ta mutunci, irin wadda suka tabbatar da sunzo gidan karamci, sun kuma tabbatar d'ansu yasamu d'iyar gidan tarbiyya,agidansu fareeda aka amshi lefen dan babanta ne zai d'aurama Sopy aure, aka had'a musu shatara ta arzik'i sukatafi, suna yabon wad'annan muta nen kirki.

Sopy tagama shirinta tsaf, tafito tana fad'in inna nashirya bari natafi kafin su cinyeni da masifarsu, bakamar aunty Nafisa sai bala'i takemin ina b'ata musu lokaci.
  Inna ta ce, "to adawo lfy, kuma aii sunfiki gsky tun yaushe suke jiranki amma kina d'aki kina lank'andi, aii mijinki yaga takansa, mutum yay ta abu kamar kwai yafashe masa aciki.
   To yi hak'uri inna bari natafi ina k'ara b'ata lokaci.
  To ki gaishesu, kicema yayar taku gobenfa sutaho da wuri dan ayi aikin cin-cin d'innan agama da wuri.
  To inna zan fad'a mata, tatafi tana dariyar inna, tunda bikinnan yamatso kullum tana kan aikin abubuwa bata ko hutawa .


🔶🔸3⃣1⃣🔸🔶

..............Da sallamarta tashiga gidan, suduka suka hauta da jaraba, aunty hauwa'u ta ce, " 'yarrainin wayo, kin zauna kinata yan kwana mu, saikace mu zai amfana, gwarama ki nutsu dan wannan mijin naki d'an kwalisa gara kije masa zam zam d'inki, ki rik'e abinki tunkafin wata takwace miki, irin wad'anna rubibinsu akeyi.
   Sopy ta tab'e baki, nidai baruwana, dan tun wurima idan wannan zancen zakumin na koma, aunty asiya matar uncle kabeer ta tuntsure da dariya, barsu d'iyata wad'annan yayun banzane zoki zauna, aunty nafisa ta ce, "karma tazauna aii ita zai amfana bamuba, hakadai sukaita tsokanar sopy tana musu shagwab'a.
   Gyarata suke kamar babu gobe, tundaga jikinta harzuwa inda ba'a fad'a🙈 sunsha gyara, zata zauna agidan auty Nafisa dan suci gaba da gyarata, tunda bawasu k'awaye garetaba wad'anda zasu takura mata.
  Bata zuwa ko'ina daga d'aki sai tsakar gida, kunji 'yar gatan auntys d'inta, wayartama ankarb'a ankashe, hankalin uncle G! Duk yatashi yanaso yaganta kodan su tattauna amma hakan tak'i samuwa.
   Ya kira uncle kabeer ya tambaya?.
   Uncle kabeer ya ce, "lafiyarta k'alau wlhy, nima haka nemanta nake amma tak'i yarda naganta, way tana wani gida b'oyo.
  Tofa, uncle G! Yafad'a, to watake b'oyemawa??.
   Uncle kabeer ya ce, "agonta mana.
   Uncle G! Yay dariya to shikenan tunda dai lfy ai da sauk'i, amma yakamata kazo gobe mu had'ufa.
   Okey to badamuwa, zuwa k'arfe hud'u zan shigo insha ALLAH.
  TO ALLAH YAKAIMU.

yau k'unshi amma babu amarya, inna sai fad'a takeyi akan b'oye Sopy amma sunk'i fito da'ita saidai subata hak'uri, can gidan aka kai mai k'unshi tamata ta'iya sosai wlhy karkuga yanda Sopy tayi k'yau kamar ba'itaba, jikinnan yasha gyara, Nadiya kad'ai tasan inda take, dan ita take kula da abinda yashafi k'awayensu na makaranta da wanda sukayi secondary tare.
   Sai a daren d'aurin aure aka dawo da sopy gidansu, inna ta rud'e daganin k'yawun da sopy tayi, sai latsa jikinta take tana fad'in kaga yara da dabara mikukaima auta na ne tayi haka?.
  Su aunty asiya sai dariya suke ma inna.
  Inna ta ce, "A lallai dole nabaku tukuyci dan gyaran dakukaima autata yayi.

MASU IYA MAGANA SUKANCE RANA BATA K'ARYA SADAI UWAR D'IYA TAJI KUNYA, to haka kuwa wannan ranar take ga uncle G! da Sopy.
   Ayau dai and'ara auren Youseef Hussein Ahmad da Safiyya Ibrahim kabeer, karkuso kuga wankan shaddar da ango yayi, yayi kyau matuk'a, da yawan d'alibansa da malamai 'yan uwansa sun halarci d'aurin auren, mutanen GURUM kuwa aii ba'a magana, matasan garinsu d'ai d'aine basu zoba, sai washe baki yake dan farin ciki wasuma bai sansuba, lallai naga taron gagarimin d'aurin aure, abin sai wanda yagani.
     Dak'yar na iya nemo muku amarya sopy, itamadai taci gayu cikin wata atamfa mai k'yau, idan natsaya bayyana muku kwalliyarta sai nacika littafin, amma dai tabbas ta had'u tamkar zata gasar sarauniyar k'yau, tana zaune itada k'awaenta agidan su fareeda, dukkanin 'yan professional writer da Zumunta sunje, sunkumayi rawar gani wajen mik'awa Sopy gudummawa, canna hango Hauwa lele😘 kusada amarya, to sopy saimuce ALLAH yasanya alkairi.
    Wajen k'arfe hud'u aka shirya amarya domin kaita garinsu uncle G!, dan sai ankaita can sun gama bikinsu, daga baya sai angonta yadawo da ita gidansu dake nan kano.
    Sopy sai kuka take, dan iyayene suka zagayeta ana mata fad'a da nasiha, irin wadda akema amare, "sai dai wasu amaren basa d'aukar irin wannan fad'an saboda kunnen k'ashinsu", to ita dai sopy da alama komai yana zama a kwakwalwarta.
    Da haka dai aka d'ungunma da amarya zuwa GURUM dake acikin k'aramar hukumar Tsanyawa, tareda gayyar 'yan uwa da abokan arzik'i, a k'awayenta Nadiya ce kawai taje, muma dai munbi ayari nida gayyar 'yan group d'ina dan kar abamu labari...................✍🏻 





💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 30~October~2016




🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM 💞




🔶🔸3⃣2⃣🔸🔶

.........A garin GURUM su Sopy sun sami tarba mai k'yau, daga dangin uncle G!, Suma sunada kirki, ananma biki aka d'ora, da daddare matasa suka warware kid'in daya bama dangin sopy sha'awa, atak'aice an dai sha shagali.
   Washe gari bayan sallar azuhur dangin sopy sukayi haramar komawa kano, bayan an k'ara yima amarya nasiha da jan kunne akan sirikanta da dangin mijinta, suka tattaro suka taho, aka baro amarya tana kwasar kuka.
   Da k'yar gwaggo ta lallasheta dan ad'akinta suka barota, daga k'arshe gwaggo ta lallab'ata tayi barici, kunga sirikan kwarai masu tattalin matan 'ya'yansu.
   Libabatu ta gyara b'angaren da su sopy zasu zauna kafin sutafi, wato b'angaren uncle G! Kenan, acan gefe yake akatange babu ruwanta da sirikanta saidai idan sun shiga, gyara sosai tayi ma b'angaren, ta amshi turaren wuta wajen gwaggo taje takunna, tak'ara da da wasu turarurrukan data gani ad'akin, azuciyarta ta ce, "oh ni liba, kaga d'akin yaya kamar na mace, nan dai tagama tafito.
   Uncle G! Kuwa bayan yagama hidimar sallamar bak'i masu tfy, saikuma yashiga sabgogin sallamar 'yan uwa da abokan arzik'i dake nan, dakuma mammaida kayayyakin da'aka aro na mutane.
    Sai gab da magriba aka maida Sopy b'angarenta, aunty hafsa da kanta ta had'a mata ruwan wanka, Sopy ta ce, "nagode aunty!, aunty hafsat tayi murmushi bakomai k'anwata jekiyi wankan, dan muma tafiya zamuyi, lubabatu nacan tana jirana, sai da safe.
  " Sopy ta ce, "to ALLAH yakaimu.
 Bayan fitar aunty hafsa Sopy tashiga wanka zuciyarta cike da tunani iri-iri, tagama wanka tafito sukayi kicib'is da lubabatu, lubabatu ta ce, "to amarya muzamu gudu gida, sai gobe nazo cin kazar amarci, kifa ragemin.
   Sopy tayi d'an murmushi ta ce, "to.
    Libabatu tana tafiya sopy tashiga d'akin, tabi d'akin da kallo babu wani tarkace, katifa ce k'atuwa an lailayeta da zanin gado, sai wardrobe ta zuba kaya itama k'arama, sai kujera doguwa a gefenta akwai firij, saikuma wani tebir da kujera agefensa cike yake da littatafai, da alama library d'in uncle G! Ne, ba laifi d'akin yayi k'yau a talauce ba a sarauceba.
   Ta zauna tashafa mai tayi kwalliya mai d'an sauk'i,  wata atamfa tasaka siket da riga, sun kama jikinta sosai, ta ja k'aramin tsaki nikam bana son kaya su matseni, amma na lura duk haka aunty hauwa'u ta d'inka min kayana.
   Haka ta zauna tana gyaran kai tana mitar d'inkunan, nace ashe Sopy tanada gashi ba laifi, dan dai tana b'oyeshine, tagama ta gyara gurin, sannan tahau sallah, bayan ta idar ta zauna agurin har aka kira sallar isha'i, ta tashi tayi.
   Ta cire hijjabin kenan tanufi waje akwatin ta dan d'aukar k'aramin hijjabi wanda baikai girman wanda tayi sallarba.
   Uncle G! Ya shigo d'akin da sallamarsa, Sopy tarikice tarasa inda zata dosa, wajen akwatin ko kuwa wajen hijjabin data gama sallah yanzu?.
    Shima uncle G! Tsaye yake kam cikin farar shadda k'al yaukam harda hula, sai bulbula k'amshi yakeyi, fuskar nan tasa fayau da annurin angwanci, ya kasa koda motsi dan d'imautuwa da surar Sopy, ya tambayi kansa? wai dama haka sopy take da diri da cikakkiyar sura ta d'aukar han kali, lallai dolene ya godema ALLAHn daya halicci wannan k'ak'yk'yawar sura.
    Ahankali ya k'arasa gareta, tasaka hanu tana kare k'irjinta🙅, ta rintse idanu danjin uncle G ya mannata da jikinsa, cak ya d'auketa ya dire saman kujera, shima ya zauna, kallonta yakeyi sama da k'asa kamar yau yafara ganinta.
   Itako kanta yana k'asa tana wasa da zoben hannunta, ta daure ta ce, "ina yini?, yaja wata sassanyar ajiyar zuciya tareda kama hannunta ya r'intse anasa.
  Jitayi tsigar jikinta ta tashi yarrrrrrr, yaune rana ta farko da namiji ya tab'a kama hannunta, ta runtse manyan idanunta.
   Uncle G! Yay murmushi, cikin muryarsa mai dad'i da amo ya ce, "kin wuni lafiya ??.
   Cikin jin kunya ta ce, "lfy law.
  Ya ce, "ya gajiyar biki??.
"Nanma saida tayi k'asa da kai sannan ta amsa.
   Ya ce, "my Sopy aii kuma kunya ta k'are yau, domin kin zama tawa nazama naki har abada.
    Ita dai tayi masa shiru, idonta arufe saboda tsananin kunyarsa datake ji, gashi kuma yak'i sakar mata hannu, ya matso da fuskarsa kusada tata, harsuna jin fitar numfashin juna, batayi aune ba taji ya manna mata wata k'yak'yk'awar sumba😘a kumatu. (Kiss)
   Tayi wata 'yar girgiza dan sumbar ta shigeta har cikin kwakwalwa......................✍🏻




💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 30~October~2016




🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷




NA BILKISA IBRAHIM 💞




🔶🔸3⃣3⃣🔸🔶

...........ya d'an murmusa dan ganin yanda taketa kare k'irjinta, yasak'ala hannunsa ta bayanta ya rungumota zuwa jikinsa, aii sai jikin mutuniyar taku ya hau rawa, cikin kunnanta ya ce, "tsawon kwana goma kina b'oyema ganina, yau kuma gani daga ni saike!!.
  Ita dai jikinta sai rawa yakeyi, takuma kasa magana, ya hura mata iska a kunnenta, ta bud'e ido da sauri, yay murmushi, Sopy sarkin kunya yafad'a yana shafa jikinta, ya kuma matseta sosai ajikinsa, har saida tayi 'yar k'ara sannan ya sassauta mata, ya ce, "haba sopy yau baza a yima uncle G!; magana bane? Ko har yanzu fushin tafiyar su uncle kabeer d'in akeyi?, dan ya ce, "min har kukayi sallama kuka kikeyi, kokuma garinmune babu dad'i??.
   Sopy ta girgiza kai alamar A'a.
 Ya ce, "to minene yasa aka k'iyimin magana??.
   Ta daure ta ce, "ba komai kainane yake d'an ciwo.
   Uncle G! Yay 'yar dariya, to ALLAH yabaki lafiya Sopy na!, amma ko dai ana tsoron uncle G! ne??.
     " nanma ta girgiza kai batare da tayi magana ba"
  Ya mik'e yana fad'in shikenan idan anzo wajen kwanciya zamu gani.
   Gaban Sopy yafad'i rasss, bata san sanda hawaye ya zubo mata ba a kumatu, tayi saurin sharewa, itakam gsky tanada tsoro, ALLAH dai yasa karyay mata komai.
   Ledar daya shigo da ita ya d'akko, wadda santin ganin surar sopy yasakashi yarda ta ak'ofar d'aki, ya zauna yana lallashinta akan taci kazar dake ciki, da k'yar yasamu taci akunya ce, yana mamakin kunya irinta sopy, gsky da haka kowace mace take, da ansamu sauk'in lalacewar 'yammata kai harma zawarawa da matan aure, ALLAH dai ya shirya.
    Bayan sun gama cin kazar wadda rabinta duk shi yaci kayansa, dan yana jin yunwa sosai, tunda aka fara bikinnan bai nutsu yaci abincin kirkiba, yaje yay brosh ya dawo, itama taje tayo.
   Ya ce, "yana zuwa yanzu zai dawo.
  Yana fita ta tashi tacanja kayan barci a gurguje, wani zani tasaka da riga tishet mara nauyi, tasaka k'aramin hijjabi, tayi kwanciyarta bisa kujera.
   Ya kai tsawon minti talatin sannan yadawo, yarufe ko ina, yabi sopy da kallo yana d'an murmushi, ahankali ya furta safiyya sarkin tsoro, shima kayan barci yasaka, yad'an fesa turare.
   Wajen kujerar datake kwance ya k'araso, ya shafa kuma tunta yana fad'in my sopy aii duk wayon amarya sai ansha manta.
   Cak ya d'auketa yana fad'in kinga gurin barcinki nan ya nuna k'irjinsa da baki, saman katifar ya direta, tana jinsa amma tayi shiru, tak'iyin ko motsi dan tsoro da kunya.
   Yashiga k'ok'arin cire mata hijjabin jikinta, sai asannan ta motsa ta rik'e hannunsa.
  Yay murmushi mai sauti ya ce, "aii dama nasan idonki biyu.
   "Tai masa shiru"
 Ya ce, "okey aii nasan maganinki, bari kiga nasan yanda zanyi kiyi magana, batayi aune ba taji bakinsa cikin nata, duk iya k'ok'arinta na ta kwace kanta amma ta kasa, ta shiga tsungu ninsa, amma ina shikam baisan tanayiba, tsotsar bakinta yake cikin zafin nama, tamkar mafa raucin zaki🐅, ayayin dayaga abinci, Sopy tun tana tsungu ninsa harta hak'ura tabarma ALLAH.
    sai da ya tsotse bakin tamkar zai rabata dashi sannan ya janye jikinsa yana maida numfashi.
  Sai a sannan Sopy tasamu bakin yin kuka.
  Ya rungumota tsam akan faffad'an k'irjinsa daketa tashin k'amshin turare, ahankali yashiga buga bayanta tamkar wata jaririya, cikin sark'ewar murya ya ce, "to kukan ya isa haka, kinga yi hak'uri ni babu abinda zan miki, yi barcinki kinji my sweet Sopy, cikin sigar lallaahi yake maganar, iska ya shiga hura mata a cikin kunne mai dad'i, ita kanta bata san sanda barci yay awon gaba da itaba, dama ga gajiyar biki.
   Shikam ya dad'e baiyi barcin ba, dan kuwa hanka linsa yakai k'ololuwar tashi, anya zai iya cika alk'awarin daya d'auka na barin Sopy har sai sun koma gidansu, yaja wani gwauron numfashi tareda sake manneta a jikinsa, sanda bashida matarma baidamu ba haka, amma yau kodan yaganta a kusa dashine oho, ya tsurama fuskarta idonu, tanata barcinta, dukda yasan barcin cikin tsoro da fargaba ta yishi, ya shafa kanta tareda sumbatar ida nunta yana murmushi Sopy sarkin tsoro yafad'a yana gyar kwanciya.
   Haka yayta sak'a wasik'ar jaki har barci yay awon gaba dashi.

Muma muka fito, dan komawa masaukinmu nida marak'isiyya, da madina, da aunty pii pii, da saratu, dan sunce ba inda zasu labari ya wucesu.
   Na ce, "magulmata saiku tsaya, nasan kuna bak'in cikin d'an abinda uncle G! Zai banine,  idan nagama yad'a labinsune, to kusani kad'an zan baku eheee😜😜😜 .....................✍🏻




💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'sala💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 2~November~2016




🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷




NA BILKISA IBRAHIM💞




🔶🔸3⃣4⃣🔸🔶

........Da asuba yatashi yay alwala sannan yatada ita ya ce, "nawuce masallaci, kanta ak'asa ta ce, "to adawo lfy. 
   Bayan fitarsa itama alwalar tayo tayi sallah, ta d'auki alkur'anin data gani a d'akin tayi karatu, zuwa sannan gari yafara haske, harzuwa sannan uncle G bai dawoba, ta tashi ta gyara d'akin fes, tashare d'an lungun nasu ta wanke bayin sannan tashiga wanka.
   Uncle G yadawo motsin dayaji abayi ya tabbatar masada tana wanka, d'akin yashiga yashaki wani k'amshi mai dad'i ya lumshe idanu, yay murmushi mai k'ayatarwa ya ce, "lallai ina son mutum mai tsafta da rashin son jiki, gashi kuma ALLAH ya azurtani da samun mace, ALLAH nagodema da irin wannan tarin ni'imomi daka min.
   Batayi zaton yana cikiba, dan haka tashigo d'akin kanta tsaye, gabanta yafad'a yayinda taga uncle G zaune, takalli jikinta daga ita sai zanifa, ta faki idonsa ta rarumi hijjabin sallah ta rufe jikinta.
    Lamarin yayi matuk'ar bawa uncle G! dariya amma saiya gimtse ya ce, "yayadai ko kina jin sanyi ne?.
  Ta ce, "A'a".
 Ya girgiza kai yana murmushi, taso wa yayi yanufo inda take, aii tunkafin yazo ta durk'ushe k'asa, ya tallafota zuwa jikinsa, saman kujera ya zauna ya d'orata saman cinyarsa ya ce, "haba autar inna aii komai na Sopy mallakin uncle G! ne, kokin manta baba da uncle kabeer sun bani har abada?.
   Ta cusa kanta cikin hijjabi, tana mamakin uncle G wai dama haka yake?, wlhy da idan aka fad'a mata haka yake zata k'aryata, amma dan ALLAH jibi abinda yayi mata jiya da daddare, tamkar ba malamin taba.
   Jin tayi shiru saiya d'an girgizata, yasa hannu yacire hijjabin daga fuskarta ya ce, "Safiyya! wannan kunyar takifa tayi yawa, nikam zata hanani shan sharafin amarci, amma bari nafara rageta, yafara k'ok'arin kwance zaninta.
    Da sauri ta rik'e hannunsa tana fad'in plz uncle!  kayi hak'uri na tuba.
  Ya tsaya yana kallonta ya ce, "to kin yarda na shafa miki mai da kaina!.
  Ta waro ido waje👀 tana kallonsa ta ce, "saikace wata jaririya?", ya lumshe manyan ida nunsa yana murmushi, aii kema jaririya tace, kafin ki haifa mana wasu jariran.
  Ta sinne kanta ak'irjinsa dan kunya.
   Sallamar dasukajine yasa ta tashi daga jikinsa, ta d'auki hijjabin tasaka, uncle G ya ce, "kowa nene yashigo, Aysha! tashigo da tire a hannu ta, ta dire sannan ta gaishesu, harta mik'e uncle G ya ce, "Aysha akwai ruwan zafi kuwa agidannan?,  zanyi wanka, ta ce, "e, yaya akwai wanda aka dafama baki na wanka, ya ce, "okey to d'auki botiki ki d'ebo min, ta ce, "to.
   Babu dad'ewa Aysha takawo masa ruwan wankan, yaje yay wanka, kafin ya fito tayi sauri ta shirya, yashigo yana fad'in sopy kedai bak'ya gajiya da hijjab ko? Murmushi kawai tayi batareda tace komaiba, ya shirya cikin k'ananun kaya, sannan sukayi karin kumallo.
   Dole ya fita don muta nen daketa zuwa ganin amarya.
   Haka rayuwa tacigaba da tafiya a Gurum sopy tana ganin soyayya wajen dangin mijinta da iyayensa, kowa sonta ya ke da son faranta mata, sai abinda takeso zata ci, uncle G kam aii yafi kowa nuna mata kulawa, kuma yanzu baya shige mata, dan yaga tana matuk"ar jin kunyarsa, shima yakula idan yaci gaba da shigemata tofa zai cutu, dan haka ya shareta ko wajen kwanciyama kaida k'afa sukeyi.
  Hakan yayima sopy dad'i kuwa, takan fita tsakar gida ta taya gwaggo aiki, da gwaggo tafara aiki ita kuma zataje ta karb'e, hakan yana k'arama gwaggo son sopy a zuciya, dan suna yabawa da halayen yarinyar itada baba.
  Da haka sati guda yacika suka fara shirin dawowa kano, saidai nakula sopy bata son dawowa dan garin yayi mata dad'i.................✍🏻



💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 2~November~ 2016



🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷




NA BILKISA IBRAHIM 💞




🔶🔸3⃣5⃣🔸🔶

.........WASHE GARI suka tashi da shirin tfy, uncle G! Yana kula da sopy bata son a tafi.
   Nasiha sosai baba da gwaggo sukai musu, dan sunce sopyma tazama d'aya daga cikin 'ya'yansu.

 " Haka yakamata surukai su rink'a d'aukar matan 'ya'yansu, bawai ki zauna kina kishi da matar d'ankiba, wannan ba dai dai bane, idan kika d'auketa d'iyarkima wlhy saitafi girmamaki da baki daraja, amma daga lokacin dakika fara kishi da ita, tofa rainine zai shiga tsakaninku, shima d'an naki yazo yana jin haushinki a baza awofi, ALLAH yasa mugane".

Sai bayan sallar azahar suka tafi sopy harda kuka, shi dariya ma take bashi, har sukazo tsanyawa tana kuka, daya kula idan ya k'yaleta ba bari zatayiba, sai ya fara janta da hira, tun tana amsawa ciki ciki harta ware tana kallon hanya da garuruwa, ya tsaya a bichi suka sha mai, sannan suka cigaba da tfy, ta ce, "to nan wane garine?, ya ce, "bichi kenan indai kinji ana fad'in bichi to itace wannan, A'a ni yauma natab'a jin sunan garin, yay murmushi kawai batareda ya ce komaiba.
   Gab da la'asar suka shiga cikin kano, ya ce, "yanzu ina kikeso mu fara zuwa? Kona kaiki ki gaida su inna?.
   Da sauri ta ce, "e, muje gidan su inna.
 Yad'an murmusa batare da ya ce komaiba.
   Ganin sun wuce titin layinsu ta ce, "munfa wuce uncle koka manta ne?, yad'an kalleta sannan ya maida kallonsa bida titi, na canja shawara ne aii.
  Saboda mi? Sopy ta tanbaya.
Ya dafe sitiyari da hannu biyu saboda naga kamar bai daceba ne, sun kaiki gidan miji kuma kin zo musu yanda suka kaiki, yakamata a samu canji.
   ALLAH sarki Sopy ita kam bata fahimci inda ya dosaba, amma ta lura kamar da wata fassara yay maganar, daga nan tayi shiru bata sake maganaba, shima dai bai kuma cewa komaiba, har suka isa anguwarsu.
   Gidan ma daidaicine, ginin talaka mai wadatar zuci, da kansa yafita ya bud'e get d'in sannan suka shiga, inda motar ta tsaya nanne kawai fili, daga ita kuwa babu abinda zai k'ara shiga koda mashin ne, suka fito ya ce, "Safiyya ga gidanki to.
  Sopy tayi 'yar dariya ta ce, "naganshi kuma yayi k'yau.
    Shima ma dariyar yayi yana bud'e but d'in motar ya sauke kayan duka, ya d'auki wasu yana fad'in namanta kefa makauniyace sai nayi miki jagora a gidan naki, itama d'auka tayi tabishi, yasa mukulli ya bud'e k'ofar falon, wani k'amshi ya daki hancinsu, suka ajiye kayan, ya ce, "zauna na k'arasa d'akkowa.
    Sopy tabi falon da kallo tana jinjina kai, lallai iyayenta sunyi k'ok'ari, falon yayi k'yau, komai acikinsa jaa da farine, kujerune set guda sai santa rok (center rug) atsakkiya kujerun shima jaa anmasa kwalliya da fararen fula woyi, sai tebir a tsakkiyarsa shima dai tare suke da kujerun, falon zagaye yake da labulaye suma jaa da fari, sai tv sitan  shima irin kujerun an d'ora filasma k'arama akai ta dai dai talaka.
   Takai dubanta a dani (dinning) shima ank'awatashi da kujeru da firij, idan bata mantaba ta dad'e da ganin kujerun dani d'innan a gidan aunty Nafisa an lillib'esu da wani k'yalle ashe natane, hawaye suka gangaro a kumatunta na dad'i, bata san da bakin da zata godema iyayentaba da yayyenta musamman ma uncle kabeer dan yafi kowa taka rawar gani acikin rayuwarta, dama yayyenta sunsha gaya mata saboda aurenta suke sana'a tabbas yau ta shaida haka.
    Uncle G! ya kamata ya zaunar saman kujera, dan tun d'azu yana kallonta, yasa hannu yana share mata hawayen fuskarta, ya ce, "Safiyya ba kuka zakiyi ba addu'a yakamata kiyima 'yan uwanki domin sun taka rawar gani a kanki, ko mak'iyi  yaga kayannan saiya jin jina musa, hannunta yakama yanufi kichin da'ita aii sai sukaga abin kallo yana kichin, lallai kicin d'innan ya tsaru nanama komai jaa aka tsara, ya ce, "ga sito d'inki ya nuna mata wata 'yar k'ofa, koda yake zomuje ki gani, suna bud'ewa kayan abinci suka bayyana uncle G! yasaki baki yana kallon ikon ALLAH harda su drinks yasan wannan tabas aikin uncle kabeer ne, uncle G ya rungume sopy cikin farinciki, ya ce sopy narasa bakin maga wlhy saidai muyita yima su baba addu'ar gamawa lfy, zomuje ki ida ganin ko ina.
   Bedroom d'inta ya kai ta, sannan sukaje nasa nanma ya had'u saidai nasa komai ruwan ganyene (green) kenan, ya zaunar da ita a bakin gadoyana fad'in Safiyya kinga gidanki sai dai k'aramine dan na talakane, a hakama nakai tsawon shekara hud'u ina ginashi, dan cikin albashi ake cire wani abu ad'anyi aikin, amma mun godema ALLAH da baiwar da yayamana ta rai da lfy, ahakama munfi wasu, ina fata zakizo mu had'a kai mu zauna kfy, mukuma yarda da k'addara aduk lokacin data riskemu, muyi hak'uri a lokacin da babu ta waywayemu, muzama masu wadatar zuci akan abinda ALLAH ya azurtamu dashi, mukuma gode masa.
   Arzik'i bashine rayuwa ba dan da wani arzik'in gara dawwama a talauci, nayi alk'awarin zan rik'eki amana, sannan ina rok'onki damuyi hak'uri da juna a yayin da muka samu sab'ani, mukuma fahimci juna alokacin da wani abu yashige mana duhu, na tabbata wannan zai taimaka mana wajen zaman aure.
   Sopy ta ce, "insha ALLAHU zaka sameni mai biyayya a gareka.
    Ya ce, "ALHAMDULILLAH.
yanzu tashi muje na rakaki d'akinki kid'an watsa ruwa ko?.
  Ta ce, "to......................✍🏻




💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 3~November~2016



🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💞



🔶🔸3⃣6⃣🔸🔶

.........Har d'akinta yarakata, bayan fitarsa takuma k'arewa d'akin kallo, sannan tashiga wanka, tai murmushi dan ganin jininta yazo, lallai tayi farinci da faruwar hakan, tayi wanka tafito sai dai matsalarta d'aya batada always to yaya kenan zatayi?, tasan daga nan zuwa dare dole ta nemi mafita, inko ba hakaba zai rink'a b'ata mata jikine, tana nan zaune tana sak'a wasik'ar jakai saitaji sallama, ta fito da sauri tana amsawa, saitaga wata 'yar matsakaiciyar budurwace hannunta rik'e da kwando.
   "Yarinyar ta gaidata."
"Ta amsa cikin sakin fuska".
    Yarinyar ta mik'o mata kwandon dake d'auke da kuloli ta ce, "gashi inji aunty Asiya.
   Sopy ta ce, "aunty Asiya kuma?, wace aunty Asiya nasani anan anguwar?.
   Uncle G yafito sanye da jallabiya fara, yarinyar ta gaidashi, saida ya amsa sannan ya ce, "Asiya matar kabeer fa, aii bamuda nisa gidansu na nan k'asanmu.
   "Lah aii ban saniba".
 Ya ce, "na mantane nagaya miki, ni bari naje masallaci lokaci yana k'ara k'urewa, ta ce, "adawo lfy, yafita yana fad'in ALLAH yasa.
   Yana fita Sopy ta Cema yarinyar ya sunanki?.
   Ta ce, "sunana fatima amma anace mini ummy, nice name sopy tafad'a.
    To ummy dan ALLAH ina zaki sayo mini always ?, ummy ta ce, "aii akwai shago nan bayanku kawo na siyo miki.
   Yauwa ngd ummy 'yar albarka, taje ta d'akko mata d'ari biyar tabata ta fad'a mata irin wanda takeso.
    Babu dad'ewa uncle G yadawo, sannan sopy tana kicin tana d'auraye inda zasuci abinci.
   A falo yazauna ya kunna tv dan anhad'a komai, wannan duk aikin uncle kabeer ne, ummy tayi sallama ta shigo, ya ce, "O, baki tafiba?, ta ce, "e, aunty ce ta aikeni.
   Okey to kawo, ta mik'a masa ledar da canji ta ce, "bari natafi zanje islamiyyane, ya ce, "to ki gaishesu kice mun gode sosai ya mik'a mata naira d'ari, ta ce, "A'a, ngd, ya ce, "karb'i aii ni nabaki, ta amsa tana godiya ta tafi.
   Ya bud'e ledar dan son ganin minene aciki, ya ce, "tofa, abinda kuma yafaru kenan, ya ajiye yana fad'in an rusa mini show d'ina kenan.
   Sopy tafito da kayan filet, ta dire a saman tebirin dake tsakkiyar falon ta ce, "ga abinci ko akai dinning?, ya sakko k'asa yana fad'in aii ak'asama zanci, dan nagaji dayawa, saida tafara zuba masa abinci ya ce, "af, nama manta yarinyar ta ce, "tawuce gama sak'onki".
    Sopy ta ce, "to, ngd".
Tagama zuba masa farar shinkafar da miya da lemon kwakwa, sai salat.
  ya ce, "kefa?, ta ce, "sai anjima, harararta yayi, ya ce, "sa hannu muci kikuma cire wannan hijjab d'in kisha iska.
   Ganin ya d'an d'aure fuska, yasata bin umarninsa, ta cire hijjabin tazauna sunacin abincin, dukda tsakura takeyi kuma a kunyace takeci, bai kuma ce mata komaiba yacigaba da kallonsa yana cin abinci.

☆☆☆☆☆☆☆☆☆
Da daddare ya tarar da ita a d'akinta tagama shirin barci harma ta kwanta, ya ce, "taso muyi sallah, saida tayi k'asa da kai sannan ta ce, "ina fashin sallah.
   Ya ce, "okey, dama ya tanbayane dan ya tabbatar.
   A zatonta d'akinsa zai kwana amma saitaga ya hawo gadon ya kwanta kusada ita, ya jawota jikinsa ya rungume, to ba yadda zatayi tunda babu damar korarsa, saita maida kanta ta kwantar akan k'irjinsa ta hau barci.

♡♡♡♡♡♡♡♡
Rayuwa mai dad'i akeyi agidan uncle G dukda har yanzu babu abinda yashiga tsakaninsu, amma suna mutunta juna kuma uncle G yana nuna mata soyayya, danma kunyarsa datakeji tana sashi k'in yimata wasu abubuwan.
   Kullum aunty Asiya saita turo mata kalar girkin daya dace tayi masa ta whatsapp, dan haka take girki mai dad'i da gamsarwa, ta kuma gyare gidan tsaf, uncle G yana jin dad'i dan yanason mutum mai tsafta, kullum sai tayi bak'i 'yan anguwar suna shigowa ganin d'aki da kuma amaryar kanta, kunsan amarya da farinjini, har yara da 'yammata ba a barsu abayaba, kuma duk wanda yazo saita kulla masa cin cin da dubulan, dan sopy bata da rowa, abokansama suna zuwa wasu harda matansu, su aunty Nafisane dai har  yanzu babu wanda yazo acikinsu, har aunty Asiya datake kusa, garama uncle kabeer yazo sau d'aya shima da daddarene, kuma bai dad'eba yatafi...............✍🏻



💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 3~November~2016



🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💞



🔶🔸3⃣7⃣🔸🔶

............yau kwananta biyu da fara sallah, amma tak'i nunawa uncle G! hakan, batayin sallah saiya fita, kokuma ta kulle d'akin sannan tayi, to gashi gobe zai koma aiki, dan hutunsa ya k'are,   suna zaune a falo suna kallon labarai sai sukaji ana kwan kwasa gida, uncle G! ya kalli agogon dake manne a bangon falon, ya ce, "to waye da darennan?, sopy ta ce, "bari naje na duba.
   Ya ce, "A'a yizamanki barinaje.
Ta ce, "to.
Yaje ya bud'e wasu 'yammatane su biyu suka gaisheshi, ya amsa fuskarsa babu walwala, dan kunsan  uncle G! A gaban 'yammata baya sakin fusaka, ya ce, "yaya dai?, ganin yanda ya had'e fuska sai suka daburce d'aya ta ce, "dama yarinyace tafita gida tun d'azu shine muke tunanin kota zo nan?.
  Ya ce, "A'a, babu kowa nan gidan.
  Sukace to mun gode saida safe.
  ALLAH yakaimu yafad'a yamaida get d'in ya rufe, ya koma cikin gida, sopy ta ce, " Suwaye? ALLAH yasa dai lafiya?.
   Uncle G! yazauna yana fad'in wasu 'yammatane wai yarinya suke nema, yarinya kuma anan gidan?, ya ce, "haka dai sukace.
   Sopy ta ce, "sudai tasuce ta kawosu zasuce, nima na fahimci haka aii.
  Wayarsa ta shiga k'ara alamar kira, ya d'auka, cikin zolaya ya ce, "surikina yagarinne?
      Uncle kabeer ya ce, "haba malam daka d'aukeni sikin aii saika kwantar da murya.
    Uncle G! yay dariya, aii dan baka kusane amma atsugunne nake yanzuma.
   dariya sukayi gaba d'aya, uncle kabeer ya ce, "sonake nace maka yakamata gobe muje wajennan damukai magana ranar.
  okey to babu damuwa saimuje, ina uwar biyu?, uncle G ya tanbaya.
   Wlhy kaganta nan tana tayimin shagwab'a kasan mai ciki sai ahankali, ina my sweet Sopy?.
   tana nan lfy gata nan kusadani.
   To kagaishemin da ita saida safe, zataji ALLAH ya kaimu goben lfy.
   Bayan ya ajiye wayar ya kalli sopy, kabeer yana gaisheki, ta turo baki cikin shagwab'a ta ce, "shine baice abaniba.
    Yanda tayi maganar saita burgeshi, ya ce, "to bari nakira shi saiku gaisa, karkiyi kuka 'yar gatan uncle kabeer, zoki karb'a wayan.
   Azatonta da gsk yakeyi, saita tashi taje wajensa, tana k'ok'arin durk'usawa k'asa, ya jawota jikinsa, yana fad'in kinga wajen zamanki nan.
  Ta ce, "to kira mini uncle d'in mu gaisa.
   Yaja hancinta aikece uncle d'in, bawani kiranshi dazanyi, tashima na aikeki, ta tashi tsaye, saida yayi mata wani shu'umin kallo sannan ya ce, "yauwa je d'akina ki d'akko min ALKUR' ANI yana nan gefen gado.
   sofy ta ce, "to, shaf tamanta shirinta, bata kuma gane manufarsa ba, tanufi d'akinsa ta d'akko Alkur'ani, ya karb'a yana wani shu'umin murmushi mai kamada na mugunta, saman tebir ya ajiye Alkur'anin ya ce, "Sopy dama kin fara sallah?.
   Gabanta ne ya fad'i rasss dan tanbayar tazo mata a bazata, ta daure ta ce, "e,  ya kwanta a kujerar yana wata 'yar dariya ta mugunta.
    Sopy ta ce, "mugu d'an masa.
Daga nan kallo suka cigaba dayi, saidai kallo d'aya zakayima sopy kagane tana cikin wani hali mai kamada tsoro.
  K'arfe goma dai dai ya mik'e yana fad'in tashi muje mu kwanta dare yayi, Sopy ta mik'e jiki a sanyaye tayi gaba yabita abaya yana mata gwalo😜.
   Bayan sun shiga d'akinta ya ce, "ki sameni a d'akina yau acan zamu kwana, yafice abinsa batareda yajira amsartaba ,  tabishi da kallo kamar zata fasa ihu.
   Ba yanda zatayi dole tayi sabon wanka tayi shirin barci, tad'an dad'e tana sak'a wasik'ar jakai, zuciyarta cike da tsoro da fargaba, ya lek'o ya ce, "wai har yanzu baki gamabane?, ta mik'e kamar wadda kwai ya fashewa a ciki.
   Ad'akinsa ya ce, "tabiya shi suyi sallah, raka'a hud'u sukayi yayta kwararo musu addu'oi, iyakar sopy ta rink'a cewa amin, ya dafa kanta yay addu'a harda 'yan kwallansa, a zuciyar sopy ta ce, "namiji da kuka?.
   Bayan sun idar ta linke sallayar, ya canja jallabiyarsa zuwa kayan bari, yajuyo yana kallonta bazaki cire hijjabin bane?, ko bakijin zafi.
    Ta d'aga kai alamar e, yay d'an murmushi a zuciyarsa ya ce,  "duk dai wayon amrya sai ansha manta, yak'araso ya zauna kusada ita yakama hijjabin ya cire, tad'an takure jikinta kamar maijin sanyi.
   Ya ce, "inga fuskarki kamar wani abu a saman idonki, ta d'ago fuska batare da wani tunaniba, ya kama fuskarta da hannu biyu yakai bakinsa kamar zai hure mata abun, bata ankaraba taji bakinsa a cikin nata, kissing d'inta yakeyi cikin kwarewa, ahankali ya kwantar da ita saman gadon, dahaka hannuwansa suka fara shiga inda baitab'a zuwaba, Sopy tafara hawaye, nidai ganin uncle G! yau dgske yake, yasa nayo waje abina, dan kar kallon kurullar yayi yawa🙈😜..................✍🏻



💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 4~November~2016



🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💞




🔶🔸3⃣8⃣🔸🔶

...........Safiyya yau anzama cikakkun mata, saidai tasha wahala sosai sai kuka takeyi, uncle G ya rugumeta yana lallashi da sa mata albarka, ya kwantar da'ita ahankali ya ce, "bari nayi wanka sai kema kiyi.
     Bayi yashiga dominyin wanka zuciyarsa cike da farinciki irin wanda baitab'a shigaba a rayuwarsa, lallai aure rahamane kuma ni'ima ne.
   Sopy taja bargo ta kudundune danjin sanyi yana shigarta, wani wahalallen barci ya d'auketa, uncle G! yafito yana fad'in my sopy tashi kiyi wankan, ganin tayi shiru saiya hawo gadon, ya yaye bargon saiyaji jikinta da zafi rau, gashi dukta jik'a filon da hawe da zufa, yad'agota zuwa jikinsa yana fad'in sorry Safiyyana, ALLAH yay miki albarka kinji, ya azurtamu da zuri'a tagari, zanin gadon yasa ya goge mata fuskarta, ya kwantar da'ita, yanufi kicin.
    Shayi ya had'o mata mai kauri, yatada ita zaune, ta ce, "itafa ta k'oshi, ya ce, "daure kisha kinji, saikisha magani mukwanta, lallab'ata yaytayi tad'ansha kad'an, ya bata magungunan zazzab'i, sannan ya rungume matarsa suka shiga barci mai dad'i.

☆♡☆♡☆♡☆♡☆♡
   Bai san yayi b'arnaba saida safe, dan sun makara, yatada ita dan tayi wanka tay sallah, amma takasa tafiya, tanayin taku d'aya taji wani azababben zafi ya ratsa har kwakwalwarta, cikin shagwab'a ta ce, "woyyo ALLAH na inna.
    Uncle G ya k'araso da sauri ya tallafota zuwa jikinsa ya ce, "yaya dai?, cikin shagwab'a ta ce, "zafi.
   D'aukarta yayi cak yakai bayi, ruwan zafi ya had'a yaymata gashi, tanata zuba masa shagwab'a, ya taimaka mata tayi wankan tsarki, sannan ya nad'ota a tawul kamar wata jaririya.
   Tana idar da sallah ta kwanta akan sallayar dan barci takeji, uncle G! yashigo da tire a hannu ya dire agabanta, sopyna tashi kiyi break saiki kwanta gaba d'aya, da k'yar ya lallab'ata taci soyayyan kwan da shayi, bai takurataba dan lallab'ata yakeyi, bayan tagama ya kwashe kayan yazo ya canja zanin gadon, sannan ya d'auketa ya maidata saman gadon taci gaba da barcinta, shima ya kwanta yarungume kayarsa suka lula duniyar barci.

Sai k'arfe d'aya da wani abu suka tashi, sopy ce tafara tashi, ta lallab'a ahankali ta gudu d'akinta, uncle G! yana kallonta yay murmushi kawai dan ganin yanda take sand'a, shima tashi yayi yashiga wanka.
   Itama sopy ad'akinta wankan tashiga, dan har yanzu jikinta ciwo yakeyi, tafito tayi kawlliya mai sauk'i tasaka doguwar riga ta atanfa, tana tsaye gaban madubi tana fesa turare uncle G! yashigo, ya rungumeta tabaya yana fad'in kingudo kin barni to gani na biyoki aii.
   Tai kasa da kai dan kunya, ta ce, "ina kwana?, lafiya law sopyna, yaya kuka?, da kiransu inna da baba.
   Hannu tasaka ta b'oye fuskarta🙈, dan takula zolayarta yakeyi, ya ce, "bari naje massalaci nadawo
   Ta ce, "to adawo lfy, karfa ki dafa komai zanzo mana da abinci, dan yau ranarkice Autar inna.
   Ita dai murmushi kawai take, amma kunya ta hanat yin magana.

Babu dad'ewa yadawo musu da abinci, lokacin sopy ta gyare gidan ta bad'eshi da k'amshi, da kansa yarink'a bata abincin, ita kuma tana zuba masa shagwab'ar datake k'ara masa sonta.
    uncle kabeer yakirashi ya ce, "subar tafiyar sai gobe.
    aii dama surikina dole abarta sai goben, dan dama zankiraka, yau babu mai ganina a waje.
   Kai mutumina saboda mi? Uncle kabeer ya tanbaya.
   A'a, basai kajiba kaidai abar kaza cikin gashinta kawai goben ma had'u.
   ALLAH yashiryaka youseef kazama marakunya yanzu.
   Uncle G yay dariya, idan yatashi ya shiryamu tare nida kai, suka tuntsure da dariya kowa yakashe wayar.

Haka uncle G yacigaba da tarairayar sopy awannan rana, komai shi yake mata, sopy ta ce, "a zuciyar wato su maza abinda suke so kenan?.😜....................✍🏻





💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 4~November~2016




🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷




NA BILKISA IBRAHIM💞




🔶🔸3⃣9⃣🔸🔶

................JAMA'A!!! yakamata mu way wayi fareeda amaryar Abdul😜,
    Saida na d'an lek'a saboda gudun jarabar ummar Abdul sannan nashiga, ba kowa atsakar gidan sai yara daketa wasa, ban kula kowa ba nashige abina, dan yaran gidan ba kunya suka cikaba, atsakar d'aki na tarar da fareeda tayi d'ai d'ai, sai dai kallo d'aya zaka mata kagano tana cikin damuwa, dan kuwa tarame tayi bak'ik'k'irin sai dogon hanci da idanuwa gwalo gwalo, sai ciki ritsitsi a gaba.
    Ta tashi da sauri dan jin sallamata, tana ganina tasa kuka yauwa bily! wlhy nayi farincikin ganinki, dan ALLAH ki taimakeni wlhy Abdul zai kasheni a gidannan, ga kowa ya tsaneni bily! plx ki taimaka min.
    Na zauna ina fad'in fareeda! wane irin taimako kikeso in miki, kindai san halin mijinki da surukarki.
  Bily! wlhy idan baku taimakeniba kasheni zasuyi yanzu haka tun jiya cikina da bayana suke ciwo amma yak'i kaini asibiti, tunda akayi bikin Safiyya! al'amura suka k'ara lalacewa, ya ce, "yanda narabashi da Safiyya! to nima bazanyi farinciki ba a gidansa, ta rushe da kuka mai tsanani.
   Kamar daga sama Abdul! yafad'o d'akin, yabini da kallon rainin hankali, wayke bily! kike kowa? Banace karna k'ara ganinki a gidannanba ne?.
   Na ce, "haba Abdul, kaiwa "ALLAH DA MANZONSA", kabari na taimakawa fareeda! kaga batada lafiya, kasan kuwa mai ciki saida kula.
   Harara ya watsa mini, cikin fushi ya ce, "wlhy idan baki bar gidannanba zan karya miki k'afar dama.
   Na zaro ido waje😳, A'a, Abdul name dazan zauna ka karya min k'afar dama, ka cuci mijina!!, kaga tafiyata, fareeda! ALLAH yabaki lafiya, nai waje.
   Abdul! yaja tsaki yana fad'in bak'ar banza kawai, na ce, "oho nagodema "ALLAH" dayayini haka, aii fari bashine k'yauba.
    Ina fita yashiga jibgar fareeda! Kamar ALLAH ya aikoshi, dan ubanki banace karna sake ganin wani naki a gidannanba, koda kud'in ubanki muka gina gidan?, dukanta yake kamar yasamu jaka, itako sai ihu takeyi, nanko jini yafara ambaliya, yau dai ansamu ummarsa tashigo wajen, ta ce, "Abdul mitayi makane?.
    Umma kibari na kashe shegiyarnan tunda iyayenta ma ba sonta sukeyiba, dak'yar umma ta karb'eta.
    Ina tsaye a k'ofar gida tausayin fareeda! duk ya cika min ciki, sainaga an kwasota kamar kayan wanki jini nata kwarara, ko numfashin kirki batayi.
    Mai adai daita suka tare, suka tafi asibiti.
  To fareeda tsuntsun d'ai da yaja ruwa shi ruwa kan doka,, kowa kuma yataka rawar wani tofa yarasa filin taka tasa,, ALLAH dai ya shirya.


☆  ☆  ☆  ☆  ☆  ☆  ☆ ☆  ☆ ☆
      Agidan uncle G! Kam Sopy sai shan tarairaya take, yanzuma suna falo zaune suna hira, kan sopy yana saman cinyar uncle G!, hannunsa na shafa gyararren gashinta daketa tashin k'amshi.
    Cikin murya mai dad'i da taushi ta ce, "uncle G!!, ya ce, "Na'am Sopyna ya akayi?, tai shiru dan tana jin shakkar fad'ar abinda ke ranta, yad'an lek'a fuskarta ya ce, "miye damuwarki amaryata?.
   Tasa hannu tarufe fuska dan jin kunya, yay 'yar dariya sopyna ai kunya ta k'are kuma, yanzu an wuce wajen, dan Safiyya! tazama youseef!, youseef! yazama safiyya! koba hakaba?.
    Ta ce, "hakane"
     Ya ce, "ato.
    Fad'imin kome kikeso indai baifi k'arfinaba zan mikishi.
  Ta ce, "komiye?.
 Ya ce, "e.
Dama maganar komawata makarntane dan ALLAH yaushe zan koma, kaga anata wuceni a karatu.
   Sai da yad'an murmusa sannan ya ce, "to, kibari saikin warke, saiki koma, tunda nima jibi zan koma aiki, hutuna ya k'are.
   Saida ta shagwb'e murya sannan ta ce, "ALLAH nifa lfy ta k'alau.
   Kai sopyna fad'i gsky dai, kecefa d'azu kikace min jikinki duk ciwo yakeyi harda kuka kuma.
   hannu tasa ta rufe fuska tana dariya, ya ce, "ato, kedai kika fad'a da kanki, dan haka kibari sai nestweek sannan mun k'ara shan amarci saiki koma.
   b'oye fuskarta tayi acinyarsa, tana fad'in kai uncle ALLAH kana bani kunya.
   Ya d'ago duskarta yana murmushi to bani kunyata sopyna.
   Ta ce, "to, bayanzuba.
Ya ce, "nikam yanzu nakeso, yay kissing d'in goshinta, ta runtse ido kam dan kuwa sumbar ta shigeta.
 Ya ce, "sopy matsoraciya mai kuka, dan ALLAH uncle kayi hakuri karka min da zafi, wayyo innata baba kazo ka taimakeni, yafad'a yana kwaikwayon muryarta.
   D'aki ta nufa da gudu, dan taga zolayar tayi yawa.
  Koda sukazo wajen kwanciya saitaita d'ari d'ari dashi, dan tsoron kar abinda yafaru jiya yasake faruwa, uncle G! ya rungumeta yana fad'in kwantar da hankalinki sopyna babu abinda zan miki barci zamuyi,    ita dai tayi shiru amma zuciyarta cike da tsoro, ya cire mata rigar barcin dake jikinta way haka yakeso sukwana.
   Bargo yaja ya lullub'esu ya cika hannuwa da🙈kundai gane, sukayi shiga barci mai dad'i...................✍🏻



Assalamu alaikum, ina mik'o d'unbin gaisuwa ga masoyana a duk inda kuke, da godiya mai tarin yawa, ngd da bibiyar books d'ina da kuke yi,  harma wad'an da suka fara karantawa yanzu, luv u oll😂😂😂👍🏻.




💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞U MY FAN's💞💞...✍🏻




💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞

[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 4~November~2016




🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷




NA BILKISA IBRAHIM💞



🔶🔸4⃣0⃣🔸🔶

.............Yau tsawon kwanan fareeda uku a asibiti, ta haihu amma d'an baizo da raiba, kuma tun randa su umma suka kaita asibitin basu sake way wayarta ba, yau kuma tana tashi tayi gamo da takarda saki uku a gefen gadonta, kuka take rurus tana dana sanin hali irin nata, yau ga wanda ta fifita akan iyayenta ya gujeta, ta raba zuminci mai dank'o da kusancin dake tsakaninta da aminiyarta  saboda Abdul, ta cutarda masoyiyarta saboda Abdul, ta yaudari abar k'aunarta saboda Abdul, taci amanar aminiyarta saboda Abdul, amma yau yarasa abinda zai saka mata dashi sai saki uku, sakin wula k'anci da toxarci, itakam ta shiga uku yanzu wazata dosa, tasan daga iyayenta har yayyenta babu mai saurarenta, tasan babu wadda suka tsana kamar ita ahalin yanzu, takuma rushewa da kuka mai tsuma rai, wata sister tashigo tana fad'in baiwar ALLAH lfy kiketa kuka haka?.
    Fareeda ta ce, "babu komai.
 Okey sister tafad'a, dama an sallamekine, dan wani mutumi yazo yabiya kud'in.
  Fareeda ta ce, "to ngd, ta had'a inata inata tabar asibitin, zuciyarta cike da bak'in ciki, dan bata san inda zata nufaba, tasan ko giyar wake tasha bazata fara zuwa gidansuba, Dan mahaifinta ya gindaya mata sharad'i akan zuwan irin wannan ranar, takuma amince saboda lokacin giyar son Abdul tana kwasarta, lokacin da idanunta suka rufe ta manta da zuwan irin wannan rana, yauga ranar tazo mata batareda taci ribar abinda ta shukaba, saima asarori data tafka marasa adadi, wanda bazasu lussafuba, haka tacigaba da tafiya tana zubar da hawaye batarda tasan inda ta dosaba, ga jiri na d'ibarta saboda yunwa dan ta manta rabonta da cin abinci, ji kake wani kuwwwwwwww kacammmmm!!!!!, wani mai mota ya b'arar da ita a titin, da sauri mai motar yafito yana salati, kan kace mi mutane sun fara taruwa a wajen, mai motar ya ce, "a taimaka masa yasakata a mota, asibiti ya nufa da'ita cikin hanzari.


♡¤¤¤¤¤♡¤¤¤¤¤♡¤¤¤¤¤¤¤♡
      Sopy tanata safa da marwa dan tun d'azu take kiran uncle G! Yak'i ya d'aga, ta kira uncle kabeer ya ce, "basa tare, aii saita k'ara rud'ewa, can taji ana kwan kwasa k'ofa tatafi da sauri ta bud'e, saitaga uncle G!, cikin matuk'ar rud'ewa ta ce, "uncle lafiya tun d'azun nake kiranka kak'i kad'aga?.
   Yad'an rungumota zuwa jikinsa yana fad'in lafiyarnan da suk'i sopyna, amma mun godema ALLAH, yasaketa yana fad'in bafa ni kad'ai bane harda bak'uwa.
   Ta ce, "bak'uwa kuma tana ina?.
  Uncle G! yad'an lek'a ya ce, "shigo mana.
    Bak'uwar ta ce, "to.
Tana shigowa sukayi arba da Sopy, cikin zaro ido😳 Sopy ta ce, "fa ree da!! Kece?.
Itama cikin matuk'ar razana da rud'ewa ta ce, "Safiyya!!, aisaita zube gurin asume.................✍🏻
   Tofa k'ak'ak'a k'ara, shin Sopy zata amince da fareeda kuwa?, ko ko itama zata koreta ne?, idan ta amince da ita zata yafemata kuwa?, shikanshi uncle G! Idan yasan wacece fareeda zai amince ta zauna dasu?, ni kad'aice mai baku wannan amsar dan haka kubiyoni......................✍🏻








💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 6~November~2016




🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💞



🔶🔸4⃣1⃣🔸🔶

...........Uncle G! Ya kalli sopy da sauri dama kinsantane?.
  Sopy ta juyar da kai gefe ta ce, "fareeda ce fa, kuma tunda naganku tare nasan ka san ko wacece, tana fad'ar haka tanufu d'aki tana hawaye.
  Ran uncle G! Ya b'aci, amma saiya danne yashiga kiran sopy! Sopy!!.
   Banza tai masa tashige d'aki cikin sauri, yarasa abinda zaiyi ga fareeda kwance a sume, gashi yakula ran sopy a b'ace yake, ruwa yad'akko ya yayyafama fareeda takawo numfashi.
   Ya ce, "sannu".
Ta ce, "yauwa, saikuma tasaki kuka yayinda tatuno abinda yafaru yanzunnan tamkar amafarki, cikin hawaye ta ce, "dan ALLAH kabarni natafi, nagode da taimakon daka min, amma ban cancanci zama gidannanba.
   Ya ce, "saboda mi zakice haka?, taja hancinta kad'an tana dubansa ta ce, "saboda bazan iya zama a k'ar kashin inuwa d'aya da safiyya ba, ina matuk'ar jin kunyarta, sannan nasan safiyya tanada hak'uri, ammafa idan tayi fushi babu mai iya sauketa.
   Ya ce, "A'a, bazan barki kitafiba, barema kunsan juna keda matata, karki damu nidai ki amince zaki zauna damu, nikuma nayi miki alk'awarin zan shawo kan safiyya harta fahimceki, yanzu tashi ki kwanta saman kujera.
    Fareeda ta ce, "to, amma nasan sopy bazata tab'a fahimta ta ba, dan ban cancanci a fahimceni ba.
   Ya ce, "karki damu ina zuwa, d'akin sopy yanufa saidai ta kulle d'akin da key, yabuga mata amma tayi burus dashi, fita yayi yazagaya wajen window d'inta yalek'a, tana zaune akan kujerar madubi, takifa kanta saman madubin tana kuka, uncle G ya ce, "ALLAH idan baki bud'e min k'ofarnanba zan matuk'ar b'ata miki rai😎, bai jira amsartaba ya zagayo, sai yatarar ta bud'e k'ofar.
    D'akin yashiga, amma yanzu takoma saman gado, ya ce, "ki tashi ki had'a mata ruwan zafi tayi wanka, kibata wasu kayan tacanja najikinta.
   Tashitai tana hawaye😭 tacika umarninsa.
   Saida yaga ta had'a sannan yakira fareeda tashiga wanka, sannan ya fita.
   Sopy ma fitowarta tayi falo tazauna, tana kuka.
   Shikam uncle G wanka yashiga, amma tunaninsa yana kan sopy, ya kula tashiga cikin damuwa dayawa, to amma mi wannan matar tayi mata haka da zafi, kodayake yaji takirata da suna fareeda, kuma yasan fareeda a cikin tarihin rayuwarta,  wannan yasa yad'an zargi wani abu, saidai kukan datakeyi yatab'a zuciyarsa, amma yasan dole saiya nuna b'acin ransa kafin tayi abinda yakeso, da wannan sake2n yagama wankan, yafito yay shirinsa cikin k'ananun kaya, yayi k'yau kamar matashin saurayi.
  Falon yafito yanufi dinning ya zauna, sopy tana zaune tana kallonsa, shima ya juwyo ya kalleta ya ce, "yau baza'a bani abincin bane??.
   Sopy ta mik'e tana zumb'ura baki😒, shidai binta kawai yake da kallo, dan dariya take bashi amma saiya gimtse, ta zuzzuba masa abincin sannan takoma falo abinta.
   Baice komaiba yahau cin abincinsa, sai dai lokaci2 yakan kalli inda sopy take, yagama ya dawo falon shima, ya ce, "kije ki kaimata abinci itama, idan tagama saitasha magingunan ta kwanta.
   Sopy tak'ara cika da haushi, amma takasa magana dan ganin yanda uncle G ya tsare gida😕, babu damar yin jayayya dashi, ta mik'e tanufi dinning tad'iba abinci tatafi d'aki.
    Uncle G ya bita da kallo shi kam tana bashi dariya, Dan haka  yad'an murmusa tareda fad'in 'yarrigima.
    Taje d'akin ta tarar fareeda tafito wankan tana zaune tana shafa mai, ko kallon inda take batayiba ta ce, "ga abincinan ya ce, "kici, idan kina kuma buk'ata ki kwanta, tai waje batarda tajira amsar fareedar ba.
    Fareeda ta bita da kallo tana zubar da hawaye masu zafi, wai yau itace da sopynta suke zama doya da manja, sopyn dabata iya barci saita ganta, sopyn dabata walwala idan bana kusada ita, sopyn dake k'aunarta da sonta, takuma matso wasu hawaye kamar ruwan sama,😭bataga laifin sopy ba, dan ko itace abinda zatayi kenan, taja abincin ta hau ci, dan tana matuk'ar jin yunwa, cin yunwa tayi masa dan andad'e ba'a had'uba 😜😜.
   A falo kuka zaman kurame aka cigaba dayi, har akan kira sallar magriba, yashirya yatafi masallaci, itama saita shiga d'akinsa domin yin sallahr,  dama basu cin abu mai nauyi da daddare, dan haka ta d'akko alkur'ani tashiga karatu har akan kira sallahr isha'i............✍🏻

[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 6~November~2016



🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💞



🔶🔸4⃣2⃣🔸🔶

.............Uncle G yadawo daga masallacin, ganin sopy bata a palon sai yayi tunanin tana d'akinta, yanufi d'akin amma bata nan, fareeda ce kawai take barci, sai yaje kichin, nanma bata nan, dan haka yanufi d'akinsa, tana zaune a bakin gado ta rabga uban tagumi, uncle G yay wata sassanyar ajiyar zuciya tareda girgiza kai.
   Kusada ita ya zauna, amma duk bata sani ba, ya jawota zuwa jikinsa, tai firgigit alamar dawowa.
  Ya ce, "haba Safiyya wane irin tunanine haka??, ta fara mutsu2n kwace jikinta tana wani zumb'uro baki.
   Ya kuma rungumeta tsam ajikonsa ya ce, "kinga yi hak'uri muyi magana ta fahimta.
   Cikin shagwab'a ta ce, "ni dai ka k'yaleni, ba fareeda ta finiba!!.
   Ya sumbaci bakinta ya ce, "ni na isa, aii youseef! sai Safiyya!, aurenmufa yafi auren zobe💍, yanzu dai tashi muyi magana.
   Ta tatashi tana wani zuzzun b'uro baki😒, yanaso yayi dariya, amma yana tsoron karya sake tunzurata, dukda haka saida yad'an dara.
   Ta ce, "O, dariyama kake min!.😏
 Ya ce, "A'a, aii ke d'ince duk kin wani burkice min!.
   Shiru tai masa, dan shima haushi yake bata😏.
   Jawota yayi suka hau kan gadon sosai suna fuskantar juna, ta rintse ido kam, dan ganin yanda ya k'ura mata idanu, yay 'yar dariya tareda had'e bakinsa da nata, soyayya mai tsafta yashiga nuna mata, yayinda lamura suka fara nisa sai tsoro yashigeta, ta tuna wahalar datasha kwana uku dasuka wuce, tafara mutsu2n kwace jikinta, amma ina tariga tazo hannu, dole ta hak'ura yaci gaba da sarrafata yanda yaso, har yakai ga zuwa inda yake kwad'ayi🙈.
    Dukda yau batasha wahala kamar ranarba, amma tad'anji jiki, bayan komai yanatsa saiya shiga tsokanarta wai matsoraciya, tasa hannu ta rufe fuska🙈.
   Yaudai tare sukai wanka, sopy tanata wani nok'e2 dan kunya, shiko gogan naku ko ajikinsa, d'akinta taje ta canja kaya, dan har yanzu fareeda barci takeyi.
    A palo ta iske uncle G!, ya ce, "Sopyna yunwa nakejifa.
   Ta ce, "yunwa kuma?.
    Ya ce, "wlhy kuwa, bakin kwashe abincinba.
  Tad'an zaro ido😳 tana fad'in yaushe naje cikinka na kwashe maka abinci?.
   Ya ce, "zona gaya miki.
  Sopy tayi dariya ta ce, "nak'i wayon".
   "Shima dariya yayi."
 Kichin taje ta had'o musu abinci mai d'an sauk'i, ya ce, "to bak'uwarmufa??.
   Saida tad'an rage fara'a sannan ta ce, "to, aii barci takeyi.
   Uncle G! ya ce, "saiki kai mata ki ajiye, idan tatashi zuwa anjima basai taciba, to, kawai ta ce, "masa".
   Bayan sun gama suka zauna kallon labarai, sai zuwa goma ya ce, "tashi muje mu kwanta kinga gobe idan ALLAH ya kaimu zan fara zuwa aiki, ta ce, "haka ne."

♡~♡~♡~♡~♡~♡~♡~♡
    Saida suka kwanta ta ce, "uncle!!.
    Ya ce, "Na'am,
Wai dan ALLAH a ina ka ga fareeda ne?.
   Saida ya rungumeta ajikinsa sannan ya ce, "kin daina fushin da nine?, ta ce, "nidama ba fushi nakeyi da kaiba aii, kawai dai rainane ya b'aci, amma kayi hak'uri bazan sakeba.
   Yay mirmushi tareda sake rungumeta sosai yana shafa bayanta, ya ce, "na hakuta sopyna, amma kinsan ban tab'a ganin fareeda ba, nadai santa a labarine kawai.
  Ta ce, "hakane".
 ya gyara kwanciyarsa zuwa rigingine, ya ce, "bayan fita ta daga gida, asibiti na nufa, dan dubo yayan faruk da baida lafiya, nafito kenan tsautsayi yasa na bige fareeda da mota akan titi, wannan yasa na d'auketa muka koma cikin asibiti, aka karb'eta da gaggawa dan a sume take, amma ""ALLAH gafurun rahimun"" sai ta farfad'o da wuri, kuma babu inda taji wani mummunan ciyo saidai d'an guggurjewa, dan haka aka sallamemu, to sainace tafad'amin gidansu na kaita, saita shiga kuka ta ce, "batada gurin zuwa, to nikuma saita bani tausayi shine nace tabani labarinta, amma saita kasa tanata kuka, nikuma ganin haka yasa nataho da'ita gida dan ta huta, sannan idan inada halin taimaka mata saina taimaka mata, kinji yanda akai muka had'u.
   Sopy taja ajiyar zuciya ta ce, "tomiyasa baka d'aga wayataba?.
  Saida ya kalleta sannan ya ce, "na barta a motane, shiyyasa banga kirankiba.
   Ta ce, "to, yanzu yakake gani zamuyi da fareeda?, dan gsky bazan iya zama da itaba.
   Ya d'an murmusa tareda jawota jikinsa ya ce, "haba sopyna nasanki mai tausayice, kiyi hak'uri mu zauna tare harta warke, sannan saimu san abinyi, ko muje mubama baba hak'uri amaida ita gidan mijinta, nasan har yanzu kina k'yaunar fareeda, ki yafe mata sopyna ALLAH yana tareda masu hak'uri.
   Ta ce, "uncle amma kasan fareeda ta cutar dani ko?, ya ce, "nasan haka sopyna amma ki daure ki yafe mata, aii wani hanin ga ALLAH baiwane.
   Ta rungumeshi itama tana 'yar dariya ta ce, "gashima ALLAH yay min canji da samun gwarzon namiji mai ilimi da k'yau, ga nasaba.
   Uncle G yad'ago fuskarta yana murmushi, ya ce, "sopyna nagode, amma taya nazama gwarzo? Tunda ban tab'a yin wani abu dazai nuna ni gwarzo bane.
   Tayi murmushi tareda b'oye fuskarta a k'irjinsa ta ce, "kaima kasan kai gwarzone.
  Cikin kunnenta ya ce, a wajen....... ya'arasa a hankali batareda najiba, ta kuma cusa kanta a kirjinsa tana fad'in nidai babu ruwana ga bily nan tana kallonmu.
  Ya ce, "aii yanzu zan koreta, dan sa idonta yayi yawa.
   🚶🏼nima sainayo waje tun kafin a koroni, nad'an lek'a fareeda naga har sannan barci takeyi, dan haka nima nataho wajen my sweet d'ina😜😜😎...............✍🏻


Kuyi hakuri jiya ba'ayi type ba.

💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 7~November~2016



🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💞




🔶🔸4⃣3⃣🔸🔶

............Washe gari dak'yar sopy ta iya b'an b'are jikinta daga na uncle G!, dan tunda sukayi sallahr asuba suka koma suka kwanta, takula zaifara wani takale2, gashi yau zai koma aiki, tasamu dai dak'yar yabarta tashiga kichin ta had'a musu break, tana cikin gyaran falo fareeda ta fito, Sopy tayi burus da ita taci gaba da aikinta.
   Fareeda ta daure ta ce, "mizan tayaki dashi sopy?.
   Batareda ta kalletaba ta ce, "kibarshi kawai nama kusa gamawa.
    Fareeda ta dage saita taya sopy aiki, Sopy ta ce, "kije ki kwanta kinsanfa bakida lafiya, fareeda tad'anyi murmushi mai ciwo ta ce, "Sopy kenan!!; karki damu da lafiyata dan nikaina batada amfani agareni, dan haka ki kawo natayaki kedai.
   Sai asannan sopy ta kalli fareeda dake hawaye, saikuma jikin sopy yay sanyi, ta tabbata har yanzu tana k'yaunar fareeda, kawai b'acin raine yahana son tasiri dakuma danneshi datakeyi.
    Fareeda ta surkushe agaban sopy tana zubar da hawaye, ta ce, "dan ALLAH Sopy ki yafe min, wlhy nayi nadamar abinda na aikata, rud'in shaid'anne kawai ya kaini ga aikata kuskure mafi girma ga Aminiyata 'yar uwata, dakuma iyayena, kuyimin kowanne irin hukunci, indai zaku huce, ki daina fushi dani plz, ta rushe da kuka mai ban tausayi.
    Sopy ta kauda kai itama tana hawaye, sunkai tsawon minti uku kowa yana kuka, sannan sopy ta d'ago fareeda ta rungumeta suka cigaba da kuka ahaka, uncle G yana tsaye yana kallonsu cikin tausayi, lallai yasan gurinnan ana k'aunar juna, shaid'anne kawai yashiga tsakanin aminan juna, har yay tasirin b'ata tsakaninsu, ganin kukan nasu bamai k'arewa bane yasa shi yin tafi, da sauri suka juyo suna kallonsa, yay murmushi mai k'ayatarwa, tareda fad'in lallai yau ranace mai tarin farinciki da tarihi, na godema ALLAH dayasa muku hak'iri azukatanku.
   Su duka murmushi suke, farida tai surin dafe kujera danjin jiri yana d'ibarta, da sauri sopy ta ruk'ota tana tambayar lfy??.
   Fareeda ta ce, "kainane, uncle G ! Ya ce, "ki kaita d'aki ta kwanta, to sopy tafad'a tana rik'eda fareeda, uncle G! yabisu da kallo yana murmushi.
  D'aki yakoma ya kwanta dan dasauran safiya, sopy kuma taci gaba da aikinta, bayan tagama tanufi d'aki danyin wanka, amma saita tarar fareeda ta gyara d'akin tsaf, sopy ta ce, "kai fareeda keda nace kizo ki kwanta ashe kina nan kina aiki.
   Fareeda tad'anyi murmushi kawai, wanka sopy tashiga ta tsantsara kwalliya cikin siket da riga na material tayi k'yau sosai, ta ce, "fareeda kema yakamata kiyi wankan dan kiji k'arfin jikinki, saiki fito muyi break, fareeda ta ce, "to.
    D'akin uncle G! tanufa, yana kwance d'ai d'ai yana barcinsa, sopy ta kalleshi tana murmushi, lallaima mutuminnan kamanta yau zakaje aiki ko?, saman gadon ta hau, tad'an jamasa hanci, ya d'an motsa, tashiga shafa kumatunsa da saje yakwanta luf luf na bak'in gashi, ahankali ya bud'e idanunsa, ta nuna masa agogonsa data d'aukko a durowar gefen gado, ya ware ido sosai dan  ganin lokaci, ya mik'e yana fad'in sopyna nakusa makara fa.
    Sopy tayi dariya tana fad'in ato hutun nan yasa kafara mantawa da makaranta, ya juyo yana kallonta, ya matso daf da ita murya kasa2 ya ce, "ba hutune yasani mantawa da makatantaba aii.
   Sopy ta lumshe ido ta bud'e ta ce, "to, miye?, yad'an rungumota gefen jikinsa ya ce, "sopyna ce ta shayar dani zuma mai d'an d'ano, harna manta da kowa da komai.
    Safiyya ta kwace jikinta tana dariya, ta ce, "uncle nidai babu ruwana ga ruwan wankanka can a bayi, bayi yanufa yana murmushi, saida yaje bakin k'ofar yajuyo yana kallonta.
   Ta ce, "miya faru kuma??, ya d'an marairaice fuska ya ce, "baza'a taimaka amin wankanba.
   Sopy ta zaro ido waje tana fad'in rufani kasayani, yanufota yana fad'in to bari na rufaki na sayaki, da gudu tafita tana dariya, shima bayin yashiga yana dariya.


A gurguje yayi break dan yakusa makara, har wajen mota sopy ta rakoshi, ya kalli motar da mamaki dan ganin an gogeta tsaf, ya ce, "Sopyna sannu da k'ok'ari, amma yaushe kikayi aikin nan??.
   Tayi murmushi ta ce, "da safen nan uncle, ya jawota jikinsa ya rungume tsam tareda sumbatar kumatunta, ya ce, "lallai nayi dace da samun mace tagari k'yak'yk'yawa mai hankali, ALLAH yay miki albarka sopyna, yabamu 'ya'ya nagari masu irin halayen nan naki.
   Tayi murmushi tareda fad'in aikafini halaye masu k'yau, nafison 'ya'yanmu subiyoka tafad'a tana rufe fuska dan kunya🙈.
    Uncle G! Yay murmushi ya ce, "sarkin kunya, ni bari nawuce dan karna makara dayawa.
   Ta ce, "to ALLAH ya tsare ya kiyayeminkai!!, ka gaida min da mutane.
    Ya ce, "amin, tareda mata hararar wasa ya ce, "ninema d'an aikenki??.
   Ta ce, "A'a nina isa na aiki my sir d'ina, kuma sarkina.
   Yay dariya, idan nadawo zaki gayamin waye sir d'in aii.
   Sopy tashige gida tana dariya, shima yaja motar yatafi yana dariya, da k'ara jin yarinyar a zuciyarsa..................✍🏻





💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 7~November~2016




🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💞



🔶🔸4⃣4⃣🔸🔶

............fareeda dake lab'e tana kallonsu sopy takoma da sauri tazauna danganin sopy tanufo palon tana dariya.
   Sopy tashigo da sallama, fareeda taisaurin kauda komai azuciyarta ta amsa cikin fara'a, sopy ta ce, "tashi muyi break ko 'yar uwa, fareeda ta ce, "to, suna break suna hira sama2, dan yanzu babu wani sabo tsakaninsu, kunsan idan karabu dazama da mutum hakan yana faruwa, bare idan sab'ani yashiga tsakaninku.
    Bayan sun gama break sopy tanufi d'akin uncle G! domin gyarawa, fareeda! ta k'urama hoton uncle G! dake palon idanu, wani kuma shida Sopy! suna murmushi, a zuciyarta ta ce, "sopy kedai kullum mai sa'a ce, inama ace............. ..., 😳nad'an zaro ido ina fad'in fareeda!! inama ace mi?????????????????.😏😏😏

Amakaranta kuwa tunda uncle G! yay fakin d'alibai sukayo caa akansa, ya fito daga motar fuskarsa cike da fara'a, sukansu d'aliban fara'ar tasa tabasu mamaki, nan dai suka shiga gaisheshi da k'ara tayasa murnar aurensa.
    Shima gidiya yayita musu da halartar d'aurin aurensa dasukayi, dakuma tanbayarsu karatunsu.
    Sukace komai nomal amma sunyi missing nasa sosai, shima ya ce, "yayi missing nasu.
  Wata ta ce, "uncle G! ina amarya safiyya!!?, saida yad'an murmusa sannan ya ce, "tana gida nabarota, wata ta ce, "bazata dawo school baneba??, ya ce, "zata dawo amma saita k'ara hutawa, gaba d'aya gurin suka sa dariya, shima yayi gaba yana dariyar.
   A office ma bata sake zaniba, dan d'alibaine sukaita yimasa cincirindon taya murna harda malamai 'yan uwansa, wasuma gulma takawosu acikin d'aliban.
   Dak'yar ya samu kansa zuwa sha biyu yashiga lecture, saidai gaba d'aya kewar sopy saita isheshi, ya kalli gurin zamanta yaga kamar zaiganta yanzu, sukansu wasu d'aliban sun harbo jirginsa, dan duk sanda ya kalli gurin daya fara ganinta saiya yi murmushi, dahaka dai yagama musu lecture d'in yafito, suka shiga gulmarsa akan kallon gurin zaman sopy dayayi tayi.
    Daga nan wani ajin yaje yagabatar da lecture, sai karfe biyar na yamma yanufo gida, cikin zumud'in son ganin sopy.

Lokacin daya iso sopy tagama gyara gidan, tayi wanka tad'au kwalliya ta d'aukar hankali, ita kanta fareeda tana mamakin yanda sopy ta ke kwalliya yanzu, suna falo suna hira taji hon d'in motarsa, da sauri tatashi taje tabud'e masa get.
   Tun yana mota yake sakar mata murmushi itama tana maida masa murtani, yay fakin takaraso bayan ta rufe get d'in, dakanta ta bud'e masa mota, maimakon yafito saiya jawota cikin motar ta zauna kan cinyarsa.
    Ya kura mata manyan idanunsa masu haske yana wani murmushi mai k'ayatarwa, ta hure masa idanu tana murmushin itama, suka tuntsure da dariya, ta ce, my uncle kadawo lfy, saida ya sumbaci kuma tunta sannan ya ce, "lfy lau nadawo, saidai zuciyata tana nan gangar jikinace a makaranta.
   Sopy tay wani far da idan ta ce, "da gsk uncle d'ina. Ya lumshe idanu cikin wani yanayi, domin farin nata yatafi da imaninsa, ya bud"e ahankali yana kallonta, sai dai yanzu idonsa yayi d'anja ya ce, "my sopy ina k'yaunarki dayawa, nakan rasa inda zansa sonki, ashe dama haka ma'abota soyayya sukeji??.
   Sopy ta shafa k'irjinsa tana fad'in nima ina sonka my uncle d'ina har nakan rasa yanda zan musalta son naka.
   Ya rungumeta tsam ajikinsa yana wani fidda numfashi dak'yar, sunkai tsawon minti biyar ahaka, sopy ta daure ta ce, "uncle mushiga ciki ko?.
    Ya d'agota yana murmushi, ahankali yace kinsan ALLAH nama manta a inda muke, sopy ta tashi daga jikinsa tana 'yar dariya, ta zagayo tad'ayan gefen ta d'auki jakarsa ta aiki, shikuma ya bud'e baya ya d'auki wata leda suka jera zuwa cikin gida.
    Fareeda tana zaune suka shigo, tai masa sannu dazuwa sannan ta gaisheshi, ya amsa cikin fara'a, ya kalli sopy yana murmushi ya ce, "ashe ma mara lafiyamu ta warke?, sopy tayi murmushi batareda tace komaiba.
    Taja hannunsa tana fad'in sir muje kayi wanka kazo kaci abinci.
   Uncle G! ya harareta ya ce, "waye sir d'in?, sopy tayi 'yar tafiya zuwa k'ofarsa sanna ta juyo ta ce, uncle G!! mana.
  Da sauri yanufota, itakuma tashige cikin d'aki tana dariya.
     Fareeda tabisu da kallo tana ayyana abubuwa dayawa azuciyarsa, ahan kali ta ce, "dama ace................saikuma tayi shiru, 😳nakuma zaro ido waje, wai ita wannan mitakeson fad'ane?????.😏😏
    Ad'aki kuwa uncle G sunata zagaya d'aki da sopy yana son kamota, amma tak'i yarda, can yasa k'afa ya tad'ota suka fad'a kan gado suna dariya, yaymata rumfa da faffad'an k'irjinsa ya ce, "waye sir d'in??.
   cikin dariya ta ce, "sorry bafa dakai nakeyiba.
   ya ce, "dawa kikeyi?, ta ce, "to d'agani zan fad'a.
   ya ce, fad'i ahaka mana.
Ta ce, "wlhy kacika nauyi zaka fasa min ciki.
Aiko yau sai dai cikin naki ya fashe dan bazan d'agakiba saikin fad'a.
   Sopy ta ce, "wayyo ALLAH na inna kizo ki taimakeni, uncle G! Ya tuntsure da dariya, aii yau saidai ki kira duk wanda zakai kira amma babu alfarma.
    Ta ce, "ALLAH kanada nauyi fa, ya ce, "kedai kika sani, batai auneba taji yana shafata, zaitai magana ya had'e bakinsa da nata, saida ya cakud'ata yanda yakeso sannan yabarta.
   Ta mik'e tana kallon kayanta dasuka cuccurkud'e, ta shagwab'e fuska tana f'ad'in duk kayimin wani iri da kaya, d'aukarta yayi cak yay bayi da ita, tanata watsal2 da bashi hak'uri, amma bai sauraretaba, yadireta a bayin yarufe.
   Ganitai ya hau cire kaya, tasa hannu ta rufe idonta, yay dariya yana fad'in k'yadai jidashi, amma yau dole kimin wanka shine hukuncinki.
     Sopy ta durkushe kasa ido arufe dan ganin ya cire kaya gaba d'aya, ruwa ya d'iba yazuba mata ajiki, ta bud'e ido da sauri tana kallonsa, yay mata gwalo😜, doledai tayi masa wanka, itama yay mata suka fito🙈............................✍🏻




💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 17~November~2016




🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷




NA BILKISA IBRAHIM💞



🔶🔸4⃣5⃣🔸🔶

.........Rayuwa mai dad'i akeyi agidan uncle G, yana nuna mata soyayya irin wadda kowace mace take buk'ata a rayuwar aurenta,.
            "dan gsky mazan mu na hausawa basu cika nunawa matansu soyayya ba, sukan fifita neman kud'i akan matansu, wani idan ba yazo biyan buk'atarsa ba, matarsa bazata tab'a rab'ar jikinsa taji dad'iba, inko tad'an rab'u jikinsa saiyace bata da kunya, gsky hakan ba dai dai bane, mu mata 'yan son soyayyane da tattali, muna son anuna kulawa akan mu, yakamata mazan mu su gyara, ba ayita nuna miki soyayya awajeba saikinzo cikin gida kiga sab'anin haka, wannan yanasa mata hange hange, ALLAH yasa mugane amin".
    
   Yauma takama weekend dan haka uncle G! yana gida, su duka suna zaune afalo har fareeda, sopy na zaune saman doguwar kujera, uncle G! yana kwance ya d'ora kansa bisa cinyarta suna kallon wani hausa film, fareeda ma na zaune a kujera mai zaman mutum d'aya, itakam ba kallon ne agabantaba, dan taraba hankalinta gida biyu, rabi a kallon tv, rabi a kallon su sopy.
    Uncle G yad'ago idanu yana kallon sopy dake shafa kansa ahankali tana kallo, yay d'an murmushi tareda saka tafin hannu ya kare idanunta daga kallon tv.
    Cikin shagwab'a ta ce, "kai uncle neman magana ko?, ta cire hannunsa ta rik'e, yay dariya tareda fad'in to aii kece naga gaba d'aya kinbama tv amanar idanuwanki, ni koma kallona ba'ayi.
   Sopy ta tuntsure da dariya ta ce, "o, kishi kake da tvn??
  Ya d'anja hancinta yana fad'in indai akan Sopyna ne tofa komaima zan iya kishi dashi.
   Sopy ta shafa sajen sa daya kwanta luf luf akan kumatunsa, suka zurama juna idanu tamkar zasu cinye kansu.
   Sopy tafara janye nata tana d'an murmushi cikin yanayin kasala, shima saiya lumshe nasa idanun yana murmushi.
    Fareeda dake kallonsu ta runtse idanu hawaye suka zubo, tai saurin sharewa da d'an kwalin kanta, tana mamakin yanda kullum Safiyya take kasan cewa asamanta, tunda take bata tab'a wuce safiyyaba, gashidai tafi sopy k'yau nesa ba kusaba, gata fara dirarriya, amma tun suna yara, sai sopy ta samu abu kafin ita tasamu, kuma kota samu saitaga na sopy yafi nata, da tana ganin idan ta samu Abdul kamar tawuce da sanin sopyn ne, amma sai sopy tazo ta auri wanda yafi Abdul komai na rayuwa, k'yawu, ilimi, kwarjini, aji, iya soyayya, da tarin abubuwa masu yawan gskg, itakam saitaga kamar batada sa'a a rayuwarta, "muguwar zuciyarta mai sakata a hanya mara b'illewa ta ce, "mata karkice haka, yakamata ki gwada sa'arki akan uncle G,😳nace, "itakuwa wannan tana cikin hankalinta😎?????.
      Ta kai kallonta garesu, ta kula sunma manta tana cikin falon, dan babu abinda sukeyi sai shan sharafin soyayyar su,   uncle G ya matso da bakinsa kusada na sopy, yana nufin suyi kiss, da idanu ta nuna masa fareeda, ya dafe goshi yana fad'in kes.
   Sopy tayi murnushi, cikin tsokana ta ce, "irinku d'aya aii.
   Yay saurin kallonta, ya ce, "dawa??.
    Tayi dariya mai k'ayatarwa ta ce, "da...........sallamar dasukajine yahanata k'arasawa, suduka suka maido kallonsu ga k'ofar.
    Su Nadiya suka shigo da sallama, su biyarne, uncle G! yatashi zaune yana fad'in lallai yau munada manyan bak'i, sannunku da zuwa.
    Sopy taje ta rungume Nadiya, da sauran yammatan, harda zaliha, suka k'araso cikin falon.
  Kowacce ta rusuna ta gaida uncke G!, ya amsa cikin fara'a, ya ce, "zuwa babu sanarwa?
   Sukayi dariya tareda fad'in aii muna son bama sopy mamakine.
    Ya mik'e yana fad'in ayko kun bata, sannunku da zuwa.
    Sopy ta dire tire agabansu, cike da kayan motsa baki, nan suka zauna anata shan hira, da labarin makaranta, fareeda dai babu abin fad'a sai binsu take da idanu.
   Zaliha! ta ce, "kai Safiyya kinyi k'yau wlhy, kodai mun samu ne??.
   Sopy! tad'an harareta cikin wasa ta ce, "kun samu me???.
   Suka tun tsure da dariya, ayeesh! ta ce, komun samu baby mana, ikilee! tai saurin cewa kema daga gani kinsan mun samu aii.
   Sopy ta ce, "kudai wlhy 'yan iskane, nidai babu ruwana.
   Ridallah! ta dafa kafad'ar sopy tana fad'in, barsu sopy!, suma nanda wani lokaci zaizo kansu aii, indai cikine, Nadiya! ta ce, bar 'yan iska, ALLAH yasa uncle G! yajisu.
   Sopy ta ce, "aii nasanma yana jinsu Nadiya.
   Gaba d'aya suka zaro idanu suna fad'in da gske yana jinmu???.
   Sopy ta tuntsure da dariya tana fad'in matsorata, nandai sukaita hirarsu da dariya, wadda fareeda tazama 'yar kallo, dan duk sun wuce da ajinta.
    Uncle G! yafito cikin k'ananun kaya yanata zabga k'amshi, sopy ta bishi da kallon tuhuma, shima ya fahimci mitake nufi, dan haka ya d'an murmusa, sannan yabi su ayeesh da kallo ya ce, "kuna nan ko har yamma??.
   Suka ce, "da anyi la'asar zamu tafi, ya ce, "okey babu damuwa harna dawo.
  Ya maida kallonsa ga sopy data had'e rai kamar zatayi kuka, ya ce, " 'yammata ya dai??, sopy ta turo baki gaba ta ce, "wai ina zaka???, yay murmushi, wajen budurwata zani hira.
    Da sauri ta kalleshi, idanunta suka ciko da kwalla ta ce, "wlhy to ban yardaba, aii kai kace yau babu inda zaka, tazo ta kwace key d'in motar, takoma saman kujera ta zauna, suko su ikilee sai kunshe dariya sukeyi.
      Ahan kali yatako yazauna kusada ita, ya sak'alo hannunsa ta bayanta ya tallafota zuwa jikinsa, ya ce, "sorry my sopy, wasa nake miki, ALLAH wajen kabeer zanje.
    Ta kalleshi tana hawaye, to kabari anjima saikaje, yasa hannu ya share mata hawayen fuskarta ya ce, "A'a kiyi hak'uri naje yanzu, tunda kunada abokan hira, nima sainaje muyi hira da uncle kabeer, aii bazan dad'eba.
   Ta kuma turo baki, amma aii cakayi sai la'asar zaka dawo, yad'n had'eta da jikinsa yana murmushi, A'a, yanzu nafasa anjima kad'an zan dawo, ta ce, "da anyi azahar, ya ce, "nayarda, ya kama hannunta yana fad'in tashi ki rakani.
     Suna fita ya rungumeta tsam ajikinsa, cikin kunnenta ya ce, "sarkin shagwab'a, kinata zuba shagwab'a agaban su Riddallah ko???.
  Ta b'oye fuskarta a k'irjinsa tana fad'in aikaine kasa nayi, ya sumbaci goshinta toshikenan saina dawo, dan idan nabiye miki bazan fitaba, yashiga mota suna dariya.
   Bayan tafiyarsa ta dawo falon, su zaliha suka shiga tsokanarta, way irin wannan shagwab'a haka, sopy ta ce, " 'yan sa ido, kwa gaji kubarmu, gaba d'aya suka shek'e da dariaya, banda fareeda data maida kanta kan tv.
    Anan suka wuni, sunsha hira sosai, dazasu tafi sopy tabasu kayan kwalliya acikin kayan  lefenta, suka tafi suna godiya, da ajandar zata shigo makaranta ranar litinin....................✍🏻

Assalamu alaikum, ina godiya ga d'umbin masoya, dasuka turo min sak'on addu'a ga sister na datake asibiti, harma wad'anda basu samu damaba, ngd sosai da addu'arku ALLAH yabar zuminci.🙏🏻  



💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 17~November~2016




🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💞




🔶🔸4⃣6⃣🔸🔶

.........yau har sopy tagama aikin gyaran gidan fareeda bata fitoba, da kuwa kullum tare sukeyi, sopy tagama aikinta tsaf batareda tayi wani tunaniba, ko neman fareedar, bayan ta kammala komai tanufi d'akinta, fareeda na kwance abinta saman gado ta k'udundune da bargo, kallo d'aya sopy tayi mata tashige bayi abinta, dan ita azatonta fareedar barci takeyi.
    Tana shiga fareeda ta mik'e, ahankali tafito tanufi dani d'in da'aka cika da kayan break, saida tabi kowanne ta bud'e taga abinda ke ciki, sannan tanufi kicin tana yatsine fuska.
   Ta fito hannunta d'auke da robar gishiri, da sauri na lab'e dan kar ta ganni, ta bud'e ta barbad'e soyayyen dan kalin dashi, ta kuma bud'e sauran ta zuba har cikin ruwan zafi, da sauri ta maida ta koma d'akin ta kwanta kamar yanda take da.
   Sopy tafito tana 'yar wak'arta ta, ta zauna tayi kwalliya mai tsari, wando da riga tasaka na fakistan, rigar tatsaya mata iya cinya, tayi k'yau sosai.
    Tana shirin fita fareeda ta tashi tana wani mik'a alamar yanzu ta tashi a barci, sopy ta kalleta tana fad'in fareeda ince dai lafiya ko??.
    Fareeda tad'an yatsina fuska ta ce, "mikika ganine sopy??.
   Sopy ta girgiza kai, babu abinda nagani, naga yau kin dad'e baki tashiba ne kawai.
   Fareeda ta zuro k'afafubta k'asa tana fad'in wlhy jiya nadad'ene ina nafikar dare shiyyasa yau namakara, na lurama har kin gama aiki ko??.
  Sopy ta jin jina kai tana murmushi, aii babu damuwa, garama da kika huta, tai waje tana fad'in ki shirya muna jiranki a falo.
   Fareeda ta rakata da harara, tana fad'in 'yar rainin wayo, aii na daina tayaki bautar gidannan, nafiso nima nashigo amatsayin matar gidan, dan bazanta wahalar banzaba.

   Sopy kuwa d'akin uncle G! tanufa, tad'an zauna gefen gadon kusada shi tana shafa fuskarsa, ahankali ya bud'e idanu akanta, suka sakarwa juna murmushi, ya mik'o mata hannunsa wai ta tadashi, takama hannunsa tana fad'in ALLAH yasa na iya tada kai uncle d'ina!, dan kayi nauyi dayawa, yajawota tafad'o jikinsa, yasa hannu biyu yay mata zobe, cikin kunnenta ya ce, "nine mai nauyin ko??.
    Ta d'ago tana kallon fuskarsa sukayi murmushi, ta sumbaci k'irjinsa, yaja wata sassanyar ajiyar zuciya tareda k'ara rungumeta.
    Cikin sanyin murya ta ce, "my youseef tashi kayi wanka ko??, yad'an lumshe idanu, cikin shagwab'a ya ce, "saidai idan zakimin da kanki??, tad'an zaro idanu waje tana fad'in nifa nayi wanka aii saina b'ata jikina.
   Ahankali yatashi da'ita zaune shima yatashi yana mata wani sihirtaccen kallo, cikin sanyin murya ya ce, "kinyi k'yau sopyna.
    Tayi murmushi tareda fad'in nagode hubbina.
   Ya ce, "woow nice name, daga yau haka za'a ringa kirana ko??, tai wani walay da idanu ta ce, "inhar kana buk'ata??.
   Ya mik'e yana fad'in aii namafi kowa buk'ata.
   Takama hannunsa suka nufi bayi, taimasa wanka fas sannan suka fito, ta shiryashi cikin k'ananun kaya, dan yau babu aiki.
    Falo suka fito sunata zabga k'amshi mai dad'i, fareeda na zaune itama taci kwalliya cikin atamfa aiket da riga, sopy tabita da kallon dan ganin kwalliyar datayi.
   Fareeda ta basar daga kallon da sopy take mata, ta d'an zamo daga kujerar ta ce, "yaya youseef ina kwana??.
   Uncle G! ya amsa da lfy lao fareeda, kin kwana lfy??.
   Ta ce, "Alhmdllih.
    Ya ce, "masha ALLAH.
 Dani suka nufa domin yin break, sopy tafara k'ok'arin had'ama uncle G break, saida ta zuba masa komai sannan ta turama fareeda kamar yanda ta saba.
   Uncle G yaja filet gabansa yana fad'in yauwa 'yar albarka, laumar farko dayayi ya kume azaune kamar gunki, dan jin wani aza babben gishi har kwa kwalwarsa, yaja kofin shayun da sauri ya kurb'a domin neman sauk'i, amma saidai kash shima shayin haka yake.
   Fareeda tana kallonsa, amma sopy bata lura da halin dayake cikiba, dan hankalinta yana kan zuba abincinta.
   Uncle G! ya d'ago idonsa dayayi d'anja yana kallon asopy, sopy ta d'ago suka had'a ido saita sakar masa murmushi, amma ganin yanda fuskarsa ta canja sai jikinta yay sanyi ta ce, "hubbina yayadai???.
    Ya daure ya ce, "ci abincin kiji.
  Ta d'iba ta kai baki, dan ita azatonta yayi dad'ine sosai, jin gishiri zauzau yasata d'agowa da sauri tana gallonsa, shima ita yake kallo, fareeda da dad'i ya kashe ta, ta d'iba takai baki, da sauri ta zubo dashi a hannunta ta ce, "Sopy yaya haka??.
     Sopy ta maido da kallonta gareta, zuciyarta sai bugawa take da sauri2, wasu hawaye masu zafi suka zubo afuskarta.
   Amamakin fareeda saitaga uncle G! ya matsa da kujerarsa kusada sopy, ya kamo hannunta ya rumtse anasa, yasa d'ayan hannun yana share mata hawayen, cikin sanyin murya ya ce, "sorry safiyya!, karki damu, aii kowa yana kuskure a rayuwarsa, tunda haka bata tab'a faruwaba dole muyi miki uzuri.
   Sopy ta kwanto da kanta saman cinyarsa tana shashshekar kuka, ta ce, "ngd uncle d'ina daka fahimceni.
   Ahankali yake buga bayanta kamar wata jaririya, ya ce, "to ya isa haka nan, kinsan bana son kukanki.
   Ta d'ago suna kallon juna, sukaima juna murmushi, yasa hannu ya kuma sharemata hawayen, ta ce, "uncle bari naje na sama mana wani abun mai sauk'i.
   Ya jin jina kai yana murmushi.
Fareeda tabisu da kallo cikin matuk'ar bak'in ciki da haushin rashin samun nasara, mik'ewa tayi tabi bayan sopyn zuwa kichin.
    Abu mai sauk'i sukayi, dukda sopy ce rabin girkin, dan fareeda bak'in ciki ya hanata yin wani aikin kirki.
    Yana zaune afalo yana kallo suka fito, ya tashi yana fad'in yauwa sannunku, dani suka zauna suna break d'in, uncle G! sai kod'a abincin yake dan sopy ta saki jikinta, dan har yanzu bata cikin walwala, wai abincin yayi dad'i, harma yafi na kullum.
  Sopy tayi murmushin k'arfin hali, ta ce, "uncle kana dai fad'ane kawai.
  Ya ce, "da gsk nakeyi sopyna, ki kuma tambayi fareeda ma, yafad'a yana kallon fareeda datakeji kamar ta tashi tabar wajen, tai saurin k'irk'iro murmushi, cikin daburcewa ta ce, "ALLAH sopy da dad'i.
   Sopy tayi murmushi ta ce, "to shikenan ngd.
 
Bayan sun gama, uncle G yafita, sopy kuma tanufi d'akinsa dan ta gyara.
   Fareeda tana zaune abin duniya duk ya isheta, dan taso ace uncle G! ya hau kan sopy da masifa, taja kwafa tana fad'in aii idan kunsan wata bakusan wataba, ta mik'e tanufi d'aki.

Sai dare uncle G! yadawo, sopy taje ta taroshi kamar yanda tasaba, suka shigo falon suna dariya, fareeda dake zaune a falon tana kallo tad'anja k'aramin tsaki, amma basujiba, tayima uncle G! sannu da zuwa, ya amsa tareda tambayarta ya gida, ta ce, "lfy lao.
     Sopy taja hannunsa suka nufi d'akinsa, tadawo ta d'aukar masa ruwa mai sanyi takai masa, ya karb'a yasha yana fad'in sannu 'yar albarka.
   Ta karb'i kofin ta ajiye tana murmushi, ta ce, "sai wanka ko?, ya ce, "e, amma fara bani ledar can dana zo da'ita.
   Ta d'akko masa, ya ce, "bud'e ki gani mana.
  Ta bud'e tana dubawa, manyan hijjabai ne guda goma, sai nik'af guda uku, ta kalleshi tana fad'in uncle wannan fa??.
   Ya ce, "nakine, dan gobe zaki koma makaranta, kuma bana buk'ata kowane wawa ya kalle mini matata, dan tawace ni kad'ai.
   Sopy tayi dariya, hubbina kishinka yayi yawa wlhy.
   Yay murmushi, oho, kodai mizakice kice, nidai bana son arink'a kallon min matata.
   Ta ce, "to ngd sosai mijina, abin k'aunata.
   Yay dariya to saka nagani!!.
Ta saka, har k'asa yakai mata, dan wasuma suna d'an jan k'asa, tasaka nik'af d'in shima, ya kalleta ya tuntsure da dariya, wai kamar ojuju.👽
   Itama dariyar tayi ta ce, "aii kaine dai ka maidani inma ojujunne.
   Ya shige bayi yana fad'in gara dai haka aii.
    Saida yay wanka ya shirya sannan sukaje falo, sukaci abinci, yau basuyi wata hira mai tsawoba suka tashi, dan sopy tana d'okin komawa makaranta gobe.
    Koda sukaje d'akinma ba barcin sukayiba, saida suka kashe juna da soyayya mai tarin lada🙈👍🏻.
   Fareeda kam ana gado anata juye juye dan babu mahad'i😜😜.................✍🏻 






💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 18~November~2016




🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💞



🔶🔸4⃣7⃣🔸🔶

..........wannan ranar tazoma Sopy cikin farin ciki, domin kallo d'aya zaka mata kagane tsantsar farin cikinta, har a dani (dinning) takasa b'oye farin cikinta.
    Uncle G! Yabita da kallo, cikin muryarsa mai taushi da amo ya ce, "Sopyna wai yau miya sakaki cikin farin ciki ne??
   Sopy tayi wani murmushi wanda yasa kuma tunta lotsawa ta ce, "hubbina ina farin ciki yau zan koma makaranta, ALLAH bazan iya misalta maka yanda nakeson karatuba.
    Ya murmusa, yana kallonta, sai kuma yad'an  had'e rai, cikin tsoro sopy ta ce, "uncle yaya dai, saida ya kurb'i tee sannan ya ce, "aii inaga sai sati nasama zaki koma, dan yau inada wani uzuri bazan shiga makaranta da wuriba.
   aii mutuniyar taku saita fashe da kuka kawai, uncle G! baisan sanda dariya ta kufce masaba, ganin haka sai sopy ta k'ara k'arfin kukanta.
    Uncle G! yataso yakama hannunta yana dariya, yad'an tsagaita da dariyar ya ce, "kinga nifa wasa nake miki sarkin shagwab'a, tashi mutafi danni na k'oshi ma, ya mik'ar da'ita yana fad'in tashi autar inna tashi karmu makara.
   Duk abunnan dasukeyi fareeda tana wajen, amma tayi kicin2 da rai😠, dan ita lamarin bai birgetaba.
   Sukace mata sai sun dawo, batareda sun jira amsartaba suka fice.
   Amota uncle G! ya ce, "Sopy!!.
  Ta ce, "na'am.
Ya ce, "inagafa yakamata mu maida fareeda gida dan su baba su san aurenta ya mutu, bai kamata mubarta annan ba batareda kowa ya saniba, kuma sainaga kwana biyunnan kamar bata cikin walwalarta.
   Sopy tad'an gyara zamanta, sannan tajuyo tana kallon uncle G! da idanunsa ke kan titi ta ce, "gsky kafad'a uncle, saidai wlhy ina fargabar zuwa gida nace fareeda tana wajenmu, dan bammanta yanada suka rabuda iyayentaba da 'yan uwanta.
   Ya d'an juyo ya kalleta tareda k'ara dafe sitiyari, ya maida kallonsa ga titi yana d'an murmushi, ya ce, " karki damu, insha ALLAHU babu abinda zai faru, kuma nasan zasuyi miki k'yak'yk'yawar fahimta.
   Sopy ta ce, "to ALLAH yasa.
  Ya danna kan motarsa cikin marantar yana fad'in amin.
   Tunda motar tashigo su Nadiya suka nufota, dan sun san harda sopy.
  Uncle G! ya juyo yana kallon sopy ya ce, "banda yawo, banda magana da maza inhar bata kama doleba.
   Sopy tayi murmushi tareda fad'in ALLAH ngd maka daka azurtani da samun miji mai tsananin kishina.
    Yay 'yar dariya shima ya ce, "ALLAH ngd maka daka bani mata mai jin maganata, suka tuntsure da dariya, a dai dai wannan lokacin ne kuma su Nadiya suka k'araso.
   Su Nadiya suka gaida uncle G! Ya amsa yana tambarsu ya gajiyar ranar, sukace aii babu wata gajiya.
   Ya ce, "to masha ALLAH, ya nuna musu sopy yana fad'in ga amanata nan nabaku, karku yarda wani abu ya tab'ata.
   Sukace to mun karb'a.
 Yay nufi office yana fad'in saikin jini.

Suma aji suka nufa, dayake sopy tasaka nik'af babu wanda yaganeta, sai wasu tsurari dasukaga sanda uncle G! ya ajiyeta amota.
    Ahaka wani malami ya shigo yay musu lecture, bayan fitarsa babu dad'ewa uncle G! yashigo, tunda yashigo idanunsa akan Sopy, wannan yasa wasu d'aliban suka zargi wani abu.
   Sopy kama duk kunya tarufeta yanda taga yawancin d'aliban sun zura mata idanu suna son su san wacece??,  dahaka yagama ya fice.
   Wad'anda suka kasa jurewa saida suka tambayi zaliha wacece? Itako ta ce, "musu matarsace safiyya.

   Bayan fitarsa yanufi office, wasu 'yammata uku dake zaune jikin wata bishiyya suka bishi da kallo, d'aya ta ce, "wai dan ALLAH khadija shi wannan malamin waye?, nakula yacika jin kansa dayawa.
    Wadda aka kira khadija ta ce, "sunansa malam youseef hussain Ahmad, amma ana kiransa uncle G!, wannan dakikeji dagani a kwai ilimi, sai girman kai, shiyyasa 'yammatan makarantar nan suka mutu akansa, shikuma yana wulak'antasu, akwai wata kairat 'yar mai kud'ice ina gaya miki, ga k'yau, ta mutu a sonsa, amma mutuminnan yayta wulak'antata, daga k'arshe ma babanta sai America ya maida ita take karatu.
   Wadda tayi tambayar ta tab'e baki, ince hala shima d'an masu kud'inne??.
   Khadija ta ce, "wlhy talakane tib'is, shegen girman kaine kawai yake d'awai niya dashi.
   D'ayar datak'i saka musu baki tun d'azu ta ce, "nikam wlhy ina son mutum mai ra"ayin kansa,  dan irin wannan auren na kwad'ayi bashida wata riba, saima raini daga dangin matar, yanzu bagashi yayi aurensaba.
    Zainab tai saurin cewa "o, dama yanada mata??.
   Khadija ta tab'e baki, yayi aure wata d'aya daya wuce, karkiga matar batada wani k'yau sosai, kullum cikin hijjabi kamar d'iyar limamai.
   Zuh'rah tayi dariya aii haka shine dai dai, dankuwa shine mutuncin d'iya mace, su wad'ancan masu ikirarin suna son nasa, dasun suturce jikinsu daya sosu, kuma aii ba k'yau bane abinda yakamata mace tayi alfahari dashi, k'yawun hali da tarbiya sune babban jigon rayuwa.
   Khadija da taji haushin maganar zuh'rah ta ce, "zainab tashi mutafi, dan nakula itama sonsa takeyi.
   Zuh'rah tayi dariya, aii uncle G! abin sone ga kowace 'ya mace, domin yahad'a dukkan abinda mace take buk'ata, kema kanki kinsha aika masa da wasik'ar soyayya, rashin amsa tayinkine yasa kikejin haushinsa, dan nasan har hotonki wlhy kin tab'a aika masa, kuma itama zainab d'in ta k'yasane shiyyasa ta tanbayi koshi waye??.
    Cikin jin haushi khadija ta ce, "banza kawai saiki saka lasifika ki fad'a, taja hannun zainab suka bar gurin.
    Zuh'rah ta tuntsure da dariya tana fad'in 'yan rainin wayo, ku k'yawunne daku?, kowacce fuska kamar d'uwawu😜.

Sopy suna zaune da Nadiya tanad'an nuna mata ayyukan da akayi bata nan, saitaji wayarta tana wringing, ta ciro a jaka ta duba, saitaga uncle G! ne, ta d'aga tana d'an murmushi.
   Ya ce, "ki sameni a office yanzu, kafin ta ce, "wani abu ya kashe.
   Nadiya ta ce, "yaya dai??.
 Sopy tad'an ya tsine fuska ta ce, "wai uncle G! ne yake kirana.
    Nadiya tayi dariya, aii sai atashi a amsa kiran mai gida.
  Sopy ta harareta Nadiya kema sokike ki koma teema ko??.
   Nadiya ta girgiza kai tana dariya.
   Sopy ta mik'e domin amsa kiran hubbin ta.
    Deexerh ta ce, "aunty bily! Badai soyayya zasu yimana a makarantaba.
   Naja hannununta ina fad'in taho mu bita dan kar abarmu abaya, sanda muka iso har sopy ta kwan kwasa k'ofar yabata izinin shiga, mukayi wuf muka shige muma.
   Uncle G! dake zaune yana rubuce2 ya d'ago yana kallon sopy, fuskarsa d'auke da murmushi, ya ce, "sama k'ofar key, muka kalli juna nida deexerh mukace asama k'ofa key kuma???.
   Sopy ta kulle k'ofar sannan ta nufeshi, deexerh ta ce, "aunty sopyn nanmafa 'yar duniyace, na d'an murmusa dan jin furucin deexerh.
   Har zata zauna a kujerar dake kallonsa ya ce, "zonan, ba musu ta je wajensa, saman cinyarsa ya jawota, yasa hannu ya d'aga nik'af d'in, ya ce, "nima da nik'af d'in za'azo wajena??.
    Sopy tayi farrr da idanu ta ce, "ba kaine kasaka dokarba, ya sumbaci lab'anta yana murmushi, to aii banda ni acikin dokar ko???.
    Sopy takai hannu ta shafa fuskarsa tana wani d'an murmushi ta ce, "to, ayi hak'uri.
    Yanda take masa maganar dakuma shafa fuskarsa saiyasa jikinsa yay sanyi, batareda yashirya ba ya had'e bakinsa da nata, yaukam ba'a bar sopy abayaba, dan itama maida murtani takeyi, wannan yasa suka d'au dogon lokaci suna kissing d'in juna, sopy ce tafara janye bakinta, suka kalli juna itadashi, idanunsa sun d'anyi jaa, tayi murmushi tareda sinne kanta a k'irjinsa.
    Ya kuma run gumeta yana murmushi, ya ce, "saida kika gama tsotseni sannan zakiji kunya?.
   Ta ce, "kai uncle kana bani kunya.
  Yayi dariya to nadaina baki kunya, dan kar gobe akasa sumbatata, ji sukayi ana kwankwasa k'ofa...
   Sopy ta tashi da sauri ta maida nik'af d'inta sannan taje ta bud'e, malam faruk ne, ta gaidashi sannan ta fice.
    Malam faruk yak'araso yana fad'in kaida waye haka??.
   Uncle G! ya kwantar da bayansa jikin kujera yana fad'in kai atunaninka nida wa zaka gani a office a rufe??.
    Malam faruk ya zauna yana dariya, ya ce, "ito, sai dai kaida safiyya amarya.
   Uncle G! ya ce, "to itace.
Malam faruk ya tuntsure da dariya, amma mutumina ALLAH ya shiryaka, soyayya har a makaranta, to mima kukeyi a office.
    Uncle G! ya ce, "duk abinda zuciyarka tabaka, to shi mukeyi d'an sa ido.
   Malam faruk yay dariya ya ce, "ALLAH dai ya shiryaka youseef amma aii kayi hak'uri dai ku koma gida.
   Uncle G! ya ce, "kai d'an iska idan babu abinda yakawoka tashi kakama gabanka, dama kazo ka katse mini jin dad'i.
    "O, wai da gsk ne??, malam faruk yafad'a.
   Suka tun tsure da dariya suduka, uncle G ya ce, "faruk kananan baka canjaba wlhy ka iya gulma kamar mace.................    ........✍🏻




💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 19~November~2016




🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💞 



🔶🔸4⃣8⃣🔸🔶

...........Akwana atashi babu wuya gurin ALLAH, yau satin Sopy d'aya da komawa makaranata, kullum takan tashi kamar yanda ta saba ta had'a musu break, idan tana da lectures d'in safe sai su tafi tareda uncle, idan kuma batada shi sai yatafi, daga baya ta bishi.
    A b'angaren fareeda kuwa tana nan tana shirya abubuwa masu yawa akan uncle G! Dan kullum tana yaudarar zuciyarta akana wataran zata iya mallakarsa amatsayin miji, na ce, "lallai kina da aiki 'yammata.
    Yauma sopy ita kad'ai ta girka abincin rana, dan fareeda ta tsiri barcin rana, Sopy bata damu da hakanba, dan dama bataso fareeda tana tayata akan aikin gidanta, tagama tsaf tagyara gidan, yau kam a d'akin uncle G! tayi wanka, tadawo d'akinta ta shirya.
    Babu dad'ewa uncle G! yadawo, dan yad'an fita, ta taroshi kamar yanda tasaba, takawo masa ruwa yasha sannan tarakashi bayi yay wanka.
   Falo suka fito domin cin abincin rana, ya ce, "wai ina fareeda ne?.
   Sopy ta ce, "tana d'aki tana barci.
  Ya jin jina kai, badai tun barcin dana fita nabarta tanayiba?.
   Sopy ta ce, "wlhy tunshine.
Baice komaiba yaja kujera ya zauna, sopy tafara zuba masa abinci, fareeda ta fito kamar an jehota, tana wani murza idanu wai ita ta tashi daga barci.
   Uncle G! ya ce, "lallai yau kinsha barci, ALLAH yasa dai lafiya??.
   Fareeda tayi wani walay da idanu sannan ta ce, lafiya lau yaa youseef.
   Yanda tayi maganar sai ya k'ona ma sopy rai, wani abu yazo ya tokare mak'oshinta, da sauri ta d'auki ruwa tasha, uncle G! ya bita da kallon mamaki ya ce, "sopy yadai??.
   Ta girgiza kai alamar bakomai, ta tura masa filet d'in abinci gabansa.
    Fareeda tayi wani d'an murmushin samun nasa, taja kula tana zuba abincin.
    Laumar farko uncle G! ya had'e rai, yad'auki ruwa da sauri ya kora, ita dai sopy kallonsa kawai takeyi, ya ajiye cokalin ya dafe kai.
   sopy ta daure ta ce, "uncle lafiya??, yad'ago idanu cikin matuk'ar b'acin rai, ya ce, "kici abincin kiji mana.
   Jiki asanyaye sopy takai lomar abinci bakinta, wani irin aza babben yaji taji na fitar hankali, ko yarabawa dasuke shan yaji bazasu iya cin abincinba.
   Sopy ta dafe kai danjin ya sara mata, cikin masifa uncle G! ya ce, "to yau kuma miye sanadi?, ranar mun d'auka a matsayin kus kure, yau kuma amatsayin mi kikeso mu d'auka, duk maitarmu bazamu iya cin wannan yajin ba, wannan wace irin rayuwace, aii da ba haka kike girkinba ko.
   Sopy ta d'ago fuska shab'e2 da hawaye ta ce, "kayi hak'uri uncle G!, nidai nasan lafiya lau nayi girkina, wlhy bansan yanda akayi yajinnan yay yawa hakaba.
    Uncle G! yaja tsaki, ya ce, "to mikike nufi?, ko kina nufin wanine yazuba miki yajin?, naga dai gidannan mu ukune kawai,   a cikinmu waye zai zuba miki yaji a abinci? .
   Gaban fareeda ya fad'i rass.
 Sopy ta share hawaye, ta ce, "inma wani yake zubamin dan yahad'ani dakai tofa na barshi da ALLAH, tana kaiwa nan tatashi ta shige d'aki.
   Suduka binta sukai da kallo, shima saiya tashi ya shige d'akinsa cikin b'acin rai.
    Fareeda tayi 'yar dariya, tana fad'in 'yan rainin hankali kwadaiji dashi, tashi tayi tanufi d'akin sopy itama.
   Sopy tana kwance kan gado tanata rusar kuka, fareeda tashigo ta zauna gefenta, cikin sanyin murya ta ce, "sopy kiyi hak'uri, haka rayuwar aure ta ke, wani lokacin ayi farinciki, wani lokacin kuma kuka, sopy ta d'ago idanunta dasukayi jajur tana kallon fareeda, fareeda ta jin jina mata kai tana fad'in sopy gsky nake gaya miki, kuma nasan kema zaki fahim ceni.
    Batareda sopy tace komaiba ta maida kanta ta kwanta.
  Fareeda ta watsa mata harara harda gwalo😜.
   
Har dare gidan babu dad'i, sopy kuma tak'i dafa komai, tak'i shiga d'akin uncle G!, shima dai tunda ya shiga bai fitoba, fareeda ce kawai take cikin walwala.
   Sallar magribace ta fitarda uncle G! waje, saida akayi isha'i ya dawo, hannunsa rik'e da ledoji, fareeda ce kawai a falon, ya bata leda d'aya ya wuce da sauran d'akinsa, fareeda ta bud'e ledan tana wani murmun mugunta, namane ciki da kayan ciye2, tako bud'e tahau cin kayanta.
   Har wajen k'arfe goma sopy tana d'aki tak'i fitowa, uncle G! dake kwance bisa gado yanata juye2, yad'anja tsaki, azuciyarsa ya ce, "wai dama haka matan suke kamar zuma, ga zak'i ga harbi, ya tashi zaune yana bin d'akin da kallo, yay d'an murmushi yayinda idanunsa suka kai akan hoton su shida sopy, sunyi matuk'ar k'yau, kowannensu yana murmushi, atake yaji zuciyarsa ta huce, ya mik'e tsam yanufi d'akin sopy, har yanzu fareeda tana falon tana kallo, kallo d'aya yay mata ya d'auke kai, ya tura k'ofar yashiga, sopy tana kwance tana jinsa.
    Ya zauna kusada ita yana shafa fuskarta, itadai tana jinsa tayi shiru, ya duk'o da fuskarsa kusada tata har sunajin saukar numfashin juna, cikin taushin murya ya ce, "haba my sopy yau ba'ayi danine?.
   Ta janye fuskarta daga kusada tasa, tana turo baki gaba😠, ya kwanto ta bayanta, yana sassanyar dariya acikin kunnenta.
   Jitai tsigar jikinta ta tashi yarrr, ya sumbaci gefen kuma tunta, ta d'ago da sauri tana kallonsa, saita murgud'a masa baki😏, yayi murmushi yana fad'in nikike murgud'awa baki?.
   Tai masa shiru, sakkowa yayi daga gadon ya d'auketa cak, fareeda tayi saurin komawa saman kujera ta zauna, sopy kuwa sai watsal2 takeyi tana kukan shagwab'a wai ya sauketa bataso.
    Ya ce, "aii saimunje d'aki kin fad'amin wanda kika murgud'awa baki.
   Ta ce, "nifa bada kai nakeba, ya ce, "daga baya kenan.
   Fareeda ta rakasu da harara tareda jan wani mugun tsaki, dan bahaka tasoba.😜😜
   Uncle G! Ya jefa sopy saman gado, yay mata runfa da faffad'an k'irjinsa, bakinsa ya had'e da nata, yashiga nuna mata soyayya mai tsaftar gske, naja hannun hauwa'u, ina fad'in kinga zomuyi waje kafin uncle G ya koramu.
    Ta ce, kai bilki ki tsaya mud'an k'ara gani mana, na zaro idanu waje ina fad'in ALLAH ya shiryaki hauwa'u, daga samun lafiyarki, ko kinaso uncle G! ya maidaki gadon asibitine?, kijama janu d'an kuka.
    Sai da komai yalafa muka koma, tarar dasu mukai yana bata nama abaki suna ta hirarsu da dariya.
    Hauwa'u ta ce, "lallai bilki mai shiga tsakanin miji da mata yana tareda kunya.
   Na ce, "wlhy kuwa hauwa'u, hannunta naja muka nufi d'akin sopy dan mugano muku halin da fareeda take ciki.
     Saman gado muka tarar da ita, tana faman jan tsaki, na jin jina kai ina fad'in lallai wannan bata gajiba, dan na kula wani abu take k'ara shiryawa.
    Hauwa'u ta ce, " 'yar wahala, ni kinga mutafi muma wajan mazajenmu karmu lalace anan.


WASHE GARI
sopy ta had'a break tsaf, ta gara gidan, saidai yau na kula kamar akwai abinda take k'ullawa, dan sai murmushi takeyi, tana shiga wanka fareeda ta fito tanufi kichin d'in.
    Sopy suka gama shirinsu tsaf da uncle G! suka fito sunata zabga k'amshi, fareeda dake zaune afalon tun d'azu ta gaida uncle G!, suka gaisa da sopy, sannan suka nufi dini domin cin abinci, farida kuma saita nufi d'aki waizata d'akko abu.
    Sopy tagama had'ama uncle G! abinci ta tura gabansa, yako ja ya hauci, sopy tatattare kulolin datai amfani dasu tanufi kichin, nayi dariya, dan nakula sopy ta kwashe abincin sune itada uncle G! acikin wata kula daban, saita bar wani a d'ayar kular, tayi alamu kamar an d'iba.
   Tana dawowa ta tarar fareeda tafito, sai dai, sai kallon uncle G! take dayake cin abincinsa cikin kwanciyar han kali harma yana lumshe idanu.
   Taja kula itama tazu, ko kallon inda take sopy batayiba taja abincin ta ta hauci.
   Fareeda dai saicin abinci take tana matse idanu, gashi babu damar magana, tunda masu gidan basuce komaiba, saima hirarsu sukeyi, sai dai zuciyarta sai tunani take akan ya akayi basuji d'anbanzan sukarin data zuba a aciki abincin ba.
   Da haka suka gama, uncle G! yafita, sopy ma tatafi d'akinsa dan ta gyara, fareeda taja abincin da uncle G! yarage taci, saitaji lafiyarshi lau, tarike kugu👯 tana fad'in wato matar nan boye musu abinci tayi kenan??.
   Sopy dake lab'e tana kallonta tayi murmushi kawai.
    Aka kwan kwasa k'ofa da sauri fareeda taje tabud'e azatonta uncle G! ne, amma saitaga su aunty Nafisa, da aunty hauwa'u, da aunty zainab yayarta, dakuma aunty Asiya matar uncle kabeer, cikin mamaki suke kallonta, itama dai cikin tsoro da fargaba take kallonsu.
   Tofa masu karatu,  koya zata kayane kuma, kukasance taredani danjin amsar tambayarku..........................✍🏻
    



💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 20~November~2016




🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💞



🔶🔸4⃣9⃣🔸🔶

..........Aunty zainab ta wankama fareeda mari, Wanda yasata zubewa awajan dafe da kumatu, cigaba tayi da dukanta tamkar uwarta, dak'yar su aunty Nafisa suka rik'eta, cikin matuk'ar b'acin rai aunty zainab ta ce, "kubarni naci uban wannan mara mutuncin, ita hartanada k'afafun zuwa gidan safiyya, saboda batada mutunci.
    Sopy tafito da sauri dan jin hayaniya, yayunta tagani tsai tsaye da alama babu lafiya.
    Aunty zainab ta tako har zuwa inda sopy take, tana fad'in wato sopy har kin farka daga magagin cin amana da yaudara irin na fareeda ko, tanuna fareeda da jini yake zuba ta hanci saboda dukan hancinta da aunty zainab d'in tayi, ta ce, "waccan dakike gani bom ce data tarwatsa rayuwarki abaya, kuma inada tabbacin yanzuma zata tarwatsa sabuwar rayuwar dakika kasance aciki, dan ita kaskace rab'u mai jini, data tsotse jinin jikinki saita barki da zallar ruwa, takama kafad'ar sopy ta girgiza tana kuka tana fad'in haba safiyya miyasa kika amince da wadda taci amanarki, miyasa kika amince da wadda tarabu da iyayenta akan d'ana miji, itace sanadin kamuwar mahaifinmu da ciyo mai muni, itace ta haddasa bak'in ciki a family namu wanda bazamu tab'a mantawa dashiba, itace tasa mutane sukema gidanmu kallon masu k'arancin tarbiya, miyasa kika yarda mak'iyyarki wadda bata sonki dan ALLAH, Aunty zainab ta durkushe awajen tana wani irin kuka mai ban tausayi, itama sopyn saita take mata baya, suka rungume juna suna kuka.
    Suma sauran sai matsar hawaye sukeyi, fareeda kam tana gefe tana jiyyar kanta, ahaka uncle G! yashigo yasamesu, ya tsaya turus yana kallonsu da mamaki.
    Dak'yar ya iya furta tambayar waye ya mutu????.
    Gaba d'ayansu suka d'ago kai suna kallonsa, sopy tazo da gudu ta shige jikinsa, ya rungemeta tsam yana lallashinta, bayan kamar minti biyar ya cirota daga jikinsa, ya ce, "Sopy miya farune wai??, ko wanine ya rasu??.
    Sopy ta girgiza kai tana hawaye, yasa hannu yana share mata hawayen yana fad'in kukan ya isa haka, fad'amin miyake faruwa??.
       Sopy ta nuna masa fareeda da hannu, fuska duk jini da alamun duka, kunsandai farin mutim, koyaya aka tab'ashi sai yanuna.
    Uncle G! yadawo da kallonsa wajen su aunty zainab, har yanzu kuka takeyi, aunty Nafisa taje ta d'agota ta rungume, tana bata hak'uri.
      
          Tsawon minti shabiyar, kowa ya nutsu, suna zazzaune a falo, harma Sopy tayi k'arfin halin kawo musu ruwa, fareeda kuma ta wanko fuskarta.
    Uncle G! yay musu sallama suka amsa, sannan yad'ora da tambayar abinda yafaru.
    Aunty Nafisa ce tasanar masa da komai, ta d'ora dafad'in, mukammu abin yabamu mamaki, dan bamuyi tunanin ganin fareeda ananba, dukda dai agida ana nemanta, saka makon mijinta yaje har gida yafad'ama iyayenmu cewa yasaketa har saki uku.
    Uncle G! yaja numfashi sanna ya d'ora da fad'a musu yanda ya samo fareeda har zuwanta gidan da zamanta, dakuma hukuncin dasuka yanke na maidata gida, amma sopy ta ce, "tana jin tsoron hakan, dan bataso akasa fahimtarta, yaci gaba da fad"in amma ina mai baku hak'uri akan kubar fareeda domin tayi nadamar abinda ta aikata, Sopy ta ce, "azuciyarta zadai tayi nan gaba, dan mai hali baya canja halinsa uncle.
   Uncle G! ya ce, "kutan bayi Safiyya tunda fareeda tazo gidannan bata tab'a aikata mana wani abu wanda bai daceba, dan haka ina rok'onku kuma ku yafe mata, kamar yanda Safiyya ta yafe mata, inada tabbacin hakan zai taimaka mata wajen k'ara samun gyaruwar halayenta, ku kuma zamo mana 'yan jagora wajen nema mata gafara gasu baba da mama.
    Aunty zainab ta ce, "ban katsekaba yaya youseef, amma nasan har yanzu fareeda batayi nadama ba, wlhy nasan tana nan tana k'ulla wasu sababbin makirce2n nata, nasan fareeda sosai, tun muna k'anana nake fuskantar mugun halinta, nasan fareeda tafi shak'uwa da Sopy fiye da kowa acikinmu, amma nafi Sopy sanin halin fareeda, dan Sopy ta yarda da fareeda, kuma batada yawan saka idanu akan d'abi'un fareedar.
    Aunty Nafisa ta ce, "A'a, zainab tunda ya ce, "tayi nadama bakuma ta tab'a aikata wani abu dazai shiga tsakaninsuba to yakamata muyafe mata, mukuma yimata addu'ar k'ara samun shiriya.
    Nandai sukaita rok'on aunty zainab har ta sakko, ta yafema fareeda, dan saida fareedar ta gurfana agabansu tana neman afuwa, Na ce, "shegiya kamar har zuciyarta.

Yaudai anan suka wuni, Sopy tayi musu abinci mai dad'i da gamsarwa, sukasha hirarsu ta yaushe gamo, sopy ta ce, "aunty Asiya yaushe zaki haihu?, Aunty Asiya tayi murmushi ta ce, "sai watan gobe Safiyya.
   Sopy ta marairaice fuska ta ce, "dan ALLAH ki lallab'i uncle kabeer yabar uncle yakaini naga su inna, dan ya ce, "wai saikin haihu zan fara fita.
    Aunty hauwa'u ta ce, "A'a bakin koma makarantaba??, Sopy ta zumb'uro baki gaba tana fad'in, to makarantar da ga ita ina nake zuwa,?.
    Dariya sosai tabasu, Aunty zainab ta ce, "aii ko autar inna saidai kiyi hak'uri, dan muma duk haka akaimana, ta ce, "tab nikam wlhy nagaji, aii zama guri d'aya tsautsayi inji kifi, suka tun tsure da dariya suna tsokanarta.
     Fareeda kuwa tana d'aki ta kume kanta, dan taji zafin dukan, zuciyarta ta ce, "karki damu fareeda dama abu mai daraja ba'a samunshi abanza, sai ansha wahala, inda zaki bini daki2 dana fad'a miki hanyoyin dazakibi ki mallaki uncle G!.
    Na ce, "hummm naga wannan 'yar akuyar har yanzu bata san inda duniya ta nufaba.
    Gani nai tana zuba murmushi, alamun karatun da zuciyar tata takaranta mata yayi mata dad'i, kuma ta karb'eshi hannu bibiyu.
    Lallai idan zaka gina ramin mugunta tofa ka ginashi gajere, dan idan aka samu kus kure tofa kaizaka fad'a ciki.

saida akayi la'asar sannan  suka tafi, tareda alkairi mai yawa daga uncle G!.
   Bayan tafiyarsu Sopy ta shiga d'akin uncle G! Yana zaune yana duba wasu books, ta zauna gefensa, ya d'ago manyan idanunsa farare tas yana kallonta, tayi masa sassanyan murmushi, ya kanne mata ido d'aya shima yana mayar mata da murtanin murmushin nata.
     Ya rufe littafin yajuyo gareta, ta ce, "hubbina ka daina karatunne??, ya jawota jikinsa yana fad'in ai idan kina guri sopyna banida lokacin komai sai naki, kin zamomin magana d'isun da kan kama zuciyata da matuk'ar sauri idan kika kusantota, idan kuma bak'ya kusa tofa zuciyata tana tareda ke, dan gangar jikina kaiwai kike barmini, yakama yatsun hannunta yana wasa dasu, yak'ara kashe murya ya ce, "Sopyna yaushe zaki bani magajinane??.
    Sopy tasaka hannu ta rufe fuska dan kunya🙈.................✍🏻




💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞 I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 20~November~2016



🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷




NA BILKISA IBRAHIM💞



🔶🔸5⃣0⃣🔸🔶

...........Uncle G! Yay murmushi yana fad'in Sopy sarkin kunya, daga tambayar baby sai aji kunya..
   Tayi k'ok'arin mik'ewa zata gudu uncle G! yakuma matseta, ta ce, hubbina aikifa zanje nayi, yaja hancinta yana fad'in ainanma aikin kikeyi, ta ce, "aikin mi nakeyi anan?, ya ce, "na bama youseef farin ciki mana.
    Sopy tayi murmushi, ta ce, "uncle wai yaushe zamuje Gurum??.
 ya ce, "kinaso mujene??.
 ta ce, "emana inaso naje na gaida su gwaggona.
   Yay murmushi to shikenan zamuje, amma kibari sainan gaba, dan su aunty hafsat sunce zasuzo ranar juma'a.
    Cikin matuk'ar farin ciki ta k'an k'ameshi, ta ce, uncle dgsk kakeyi dan ALLAH?.
    YA CE, dgsk Sopyna, sunce zasuzo suyimana kwana biyu, ta ce, harda Aysha?, ya ce, eh harda ita.
   Kai wlhy naji dad'i sosai, tatashi tana fad'in bari kaga naje nafara shiri.
   Ya bita da kallo yana murmushi, akullum tamkar k'ara masa son Sopy akeyi, yakanji kamar babu mata aduniya sai ita kad'ai, komai na yarinyar abin sone.

^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^
Akwana atashi babu wuya gurun mai duka, komai yana tafiya yanda akeso, Sopy tana samun farin ciki awajen mijinta, takanji babu yashi a rayuwarta.
   To shima a b'anfarensa yakanji babu tankar Safiyyar, kullum burubsu su farantawa juba, takan tsara masa abinci mai gam sarwa dasaka nishad'i, kullum tana cikin kwalliya ta d'aukar hankali, ta bad'e gidanta da jikinta da k'amshi, kullum burunta tayaya zata farantawa mijinta.
   Bata wasa da samo hanyoyin rik'e miji, dan haka bily ta sakata a groups masu dama, takan tsinci abubuwan k'aruwa acikin HAUSA NOVELs masu yawa, dan kowa da irin baiwar rubutun da ALLAH yabashi, idan dare yayi su kashe junansu da soyayya itada HUBBIN ta.
    Uncle G! yana matuk'ar alfahari da ita.
    Matsala d'aya take fuskanta, itace fareeda, dan yanzu fareedar tafito dawasu salo2 na rainin hankali, sai lokacin data fuskanci sun kusa dawowa saita ci kwalliya ta zauna a tsakar gida, da sun dawo itace zata bud'e musu get tana kwar kwasa, suna shigowa falo zatayi saurin kawoma uncle G! ruwa ko lemo, da daddare kuwa tana nane dasu a falo, har saitaga sun shiga sannan take tashi, takan k'ir k'iri dafa wani abu takawoma uncle G! wai yaci, idan suna hira, taringa wata kwar kwasa da kwantar da murya kamar tana kusada mijinta,ko sopy ta gwaleta tofa bata nuna jin haushinta, wani rainin hankali kuma data d'auka shine datayi isha'i saitayi shiri cikin kayan barci tazo ta zauna falo suna hira.
   Wannan lamari yana k'ona zuciyar Safiyya.

    Yauma suna falo suna hira, uncle G! yana kwance saman doguwar kujera, yayinda sopy take zaune a k'asa saitin kansa tana cin tuffa (Apple), fareeda kuma tana saman kujera tana satar kallon uncle G!, wandashi bama ta isheshi kalloba, sopy tana kula da ita.
    Zuwa can sopy ta ce, "wayyo ALLAH hubbina??, uncle G! ya juyo da sauri yana kallonta, ya ce, "ya akayi Sopyna?, cikin shagwab'a ta ce, "jinayi kaina ya sara.
    Ya tashi zaune yana fad'in zona yimiki kamu, dan bana son kisha magani, saboda gudun ganganci, bansaniba ko nayi ajiyar baby.
    Sopy ta mike da nufin zama kusa dashi, amma saiya jawota saman cinyarsa, ta ce, "ngd hubbina.
   Yayi murmushi yana fad'in wannan aikinane, addu'a yafara yi yana tofa mata, bayan ya gama tawani kanne masa ido d'aya tareda d'aga masa gira.
   Aii sai jikin mutumin  naku yasaki, kwata2 ya manta da wata fareeda afalon, saiya had'e bakinsa da nata, yashiga sumba tarta cikin nuna kwarewa, Sopy saita bada kai bori yahau, sunkai tsawon lokaci suna abu d'aya, zuwa can yashiga shafata.
    Wani kududun bak'in ciki yatokare zuciya fareeda, ta had"iye wani mugun yawu wanda yasakata sark'ewa tafara tari.
    Sai a sanna uncle G! yatuna akwai wata halitta fareeda a falon, suduka suka d'ago suna kallonta, sopy tayi wani murmushi mugunta, tad'aga yatsun hannunta biyu tama fareeda sorry, cikin wani murmushin rainin hankali ta ce, "sorry fareedana, munata soyayya agabanki, kinsan hubbina ya iya mantar dani duniyar dana ke ciki, wlhy nama manta kinanan, ta sumbaci hannun uncle G! sukaima juna murmushi.
    Jin kalamun sopy na rainin wayo sai suka saka zuciyar fareeda kumburo wa, jita ke mar zata fashe, har fuskarta saida ta nuna alamun b'acinrai.
    Sopy ta ce, "hubbina?
Uncle G' ya ce, "na'am sopyna.
               Ta ce, "yakamata kasiyoma fareeda tv sai asaka mata a d'akina, dan bai kamata tana zama damu a falo muna tayar mata da hankaliba, kasan gwauro bai iya shiga matsalaba, gashi kuma babu mai taimaka mata😆😜.
    Uncle G! ya sumbaci bakin sopy ya ce, "gsky ne sopyna, insha ALLAHU zanyi k'ok'arin hakan, dan nima nakula tana shiga damuwa da takura.
     Fareeda tak'ara kumewa dajin kalamun sopy da uncle G!, ta kulama sun raina mata hankali, da sauri tatashi tana hawaye ta shige d'akin sopy.
   Sopy ta bita da kallo tana 'yar dariya, ta mik'e tana fad'in hubbina bari najiyo miye damuwar "AMINIYATA!!!!!;".
   Uncle G yabita da kallo yana murmushi, yasani sarai bak'ak'en magan ganu sopyn tagawa fareeda.
    A can kuwa sopy tana isa tabud'e d'akin ta shiga, agado ta tarar da fareeda tana kuka, sopy tad'an tab'e baki sannan ta k'arasa gaban gadon tana tafa hannuwa, ta ce, "fareeda kenan nakula ke har yanzu d'aukata kike amatsayin safiyya sakarai, fareeda!! Tabas abaya kinyi nasarar kwace Abdul daga hannuna, to ki d'auka awanna lokacin kece kikayi winning d'in game d'in, nikuma nasamu game over.
    Amma saidaifa awannan karon ta canja zani, domin nima da shirina nazo fagen famar, kisa azuciyarki uncle G! nawane nikad'ai, babu wata kucakar mace data isa naraba son youseef da ita, karki d'auka wani ban k'aro k'irjinki da saka kayan barci kizauna agabansa zai ja hankalinsa a kanki, 'yammatan dasuka fiki ilimi da wayewa ma sunyi abinda yafi haka amma basuci nasaraba.
   To kema inaso ki d'auka aranki bazaki tab'a yin nasaraba, tuni nasan kece kike zubamin gshiri, yaji, sukari acikin abinci, fareeda son gsky babu abinda yake rusashi, nida uncle G! son gsky mukema juna bana sha'awa ba, dan haka ki daina wahalar da kanki wajen hangen zaki iya rusa wannan soyayyar, bare harki samu damar mallakar mijina.
    Sopy tayi wata 'yar dariyar k'eta, ta ce, "lallai yau nayarda da batun aunty zainab, datace ke kaskace rab'u mai jini, kuma ke bom ce, tofa saidai ki d'auka awannan karon remote d'in bom d'inki yana hannuna, idan nagadama saina danna ki tarwatse, dan haka ki dawo da han kalinki jikinki, tun kafin kiyi asararsa, ki daina biyema shed'aniyar zuciyarki datake d'ora miki karatun da babu fassara, inko ba hakaba kina gab dashiga makarantar dana sani.
   Tana kaiwa nan tafice abinta.
 
Fareeda tana kwance kamar gunki, zuciyarta cike da mamakin kalam safiyya, wai yaushe sopyn ta waye?, ya akayima tagano sirrikan zuciyarta haka?, lallai yau sopy tagaya mata magan ganu masu ciwon gsk, irin wanda babu wani mahaluki daya tab'a gaya mata kwatan kwacinsu, ta dun k'ule hannu ta naushi iska, da sauri nafito ina tuntsura dariya😆😆😆😆😆, dan karta maujeni nima, tabar mijina da jinya.  
    D'akin uncle G! na nufa, amma saina tarar sun rufe k'ofa, dan haka na nufi hanyar fita, dan bazan koma wajen fareeda 'yar mahakaciya ba ta bibbigeni abanza, gobe nakasa kawo muku rahoto😜😜......................✍🏻



Assalamu alaikum, ina mik'o d'umbin gaisuwa ga dandazon makaranta littafin ""NI DA AMINIYATA!!!,""  ina muku fatan alkairi a duk inda kuke, ina kuma gdy da k'aunar da kuke nuna mini,, ALLAH  yabarmu tare, ya had'amu a ALJANNARSA baki d'aya.

   👌🏻acigaba da gashi😂!!!!!!!!!!!!!!!!...👌🏻



💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 21~November~2016




🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💞



🔶🔸5⃣1⃣🔸🔶

...........WASHE GARI. Fareeda kasa fitowa tayi, har sukayi break bata fitoba, Uncle G! ya ce, "Sopy yau kuwa lafiya naga fareeda bata fitoba??.
    Sopy tad'an murmusa tareda fad'in lafiyarta k'alau, k'ila ta k'oshine.
    Uncle G! yad'an tsura mata idanuwa, domin son gano wani abu, amma sai Sopy ta kauda kai tana dariya, shima saiyayi dariyar ya ce, "miya baki dariya sopyna?.
    Sopy ta ce, "kaine kabani dariya, dan naga ka kafeni da kallo kamar a kotu.
    Ya ce, "Sopyna baki da dama kema, nakula randa natashi k'ara aure zamusha fama, dan kinada kishi, ya k'arasa maganar cikin tsokana.
   Sopy ta d'aure fuska tamau.
    Uncle G! ya tuntsure da dariya, harda buga kai, yadawo kusada ita, yadafa kafad'ar ta kinga sopyna dawasa nake miki, ke kad'aice matar youseef daga ke babu k'ari.
    Sopy tad'an turo baki tana fad'in nidai ban yardaba.
   Ya jawota zuwa jikinsa ya ce, "mikike so nayi miki dan ki yarda??, ta d'ago tana kallonsa, ta ce, "kayimini alk'awari.
    Yad'an kafa mata idanu na tsawon minti biyu, saikuma ya lumshe idanunsa ya bud'e, ya jinjina kai yana fad'in ni youseef nayi alk'awarin kasancewa da safiyya har k'arshen rayuwata, kuma ita kad'ai amatsayin matata, saidai idan wata k'addara ko jarabawa takawo sab'anin haka a rayuwarmu.
    Sopy ta rungumeshi  tana murmushi, ta ce, "nima hakan take a gareni hubbina, ALLAH kuma yabamu ikon ruk'e junanamu da hak'uri da juriya.
   Uncle G! ya rungumeta yana fad'in amin ya Rabbi sopyna.

Zan iya cemuku dai ayanzu fareeda tad'an fara shiga hankalinta, dan tad'an rage aikata wasu abubuwan saidaifa har yanzu tanan akan bakanta nason mallakar uncle G! amatsayin miji, to itamadai safiyya tanan tana tanadar manya2 makaman yak'ar fareeda, dankuwa kulum tana tashi da shirin kota kwana.

Yaukam sai k'arfe biyu sopy tashiga makaranta, dan batada lecture d'in safe, sai sauri take dan tasan uncle G! yau zaimusu lecture karfe biyu da kwata, cikin sassarfa ta isa class, amma saidai ta makaro, domin kuwa har uncle G! ya shiga.
    Taja birki ak'ofar class d'in kamar yanda makararu suke tsaye, tofa saimuce kallon ya koma sama, sai hankalin 'yan class d'in da makararru suka dawo kanta, kowa yana so yaga ikon ALLAH, jiyayi k'amshin turarenta ya yawauta agurin dan haka yad'an juyo ya kalli inda yake zaton take, sukaima juna kallon ido cikin ido, amma sai uncle G! ya basar yacigaba da lecture d'insa.
    Wani k'ududun bak'in cikin ya tokare mak'ogwaron sopy, gashi gabad'aya hankalin d'aliban yana kanta.
    Uncle G! ya juyo ya kalleta yana wani d'an murmushin mugunta, dukada fuskarta tana yane da nikaf wannan bai hanata murgud'a masa bakiba, ya maida kallonsa ga d'alibai fuskarsa d'auke da murmushi.
     Bayan ya kammala lecture d'in ya fito, hannun sopy yakama batareda yayi mata maganaba, sopy tayi k'ok'arin kwace hannunta, amma saita kasa, dan ba rik'on wasa yay mataba.
    Har cikin office d'insa ya kaita, sannan yasaki hannunta yajiginna da k'ofar ya hard'e hannayensa a k'irji.
   Sopy ta kauda kai gefe dan haushi, hannu yasa ya yaye mata nik'af d'in fuskarta, ta galla masa harar tana murugud'a baki😏, yasa yatsu biyu ya kamo lab'b'anta, yad'an matsesu waje d'aya, ta rik'e hannunsa tana k'ara, dan taji zafi.
    Uncle G! ya ce, "o, autar inna da zafine??, ta harareshi da idanuwanta dasukayi jaa, yasaki bakinta yana murmushi, hannu yasa ya d'ago fuskarta suna kallon juna, ya ce, "wannan shine gargad'inki, daga yau idan kika sake makara tofa hukuncin yafi haka yawa.
    Ta lumshe idanunta, wasu hawaye suka zubo bisa kuma tunta, wani tsadadden murmushi yasaki tareda sumbatar bakinta, ta bud'e idanu da sauri, suka zubama juna ido, daka gansu kasan kallon k'auna sukema juna, suka lumshe idanu alokaci d'aya kum suka bud'e, uncle G! ya rungumeta tsam zuwa jikinsa.
    Sopy ta ce, "a zuciyarta, uncle G! Kenan,  zuma ga zak'i ga harbi👌🏻.
   
  Yau takasance juma'a, yaune kuma su aunty Hafsat zasuzo, gaba d'aya sopy ta rikita kanta sai aiki takeyi, domin tarbar bak'inta, ita dai fareeda sai kallon ikon ALLAH takeyi, hakama uncle G! binta kawai yake da kallon mamaki, dan ganin yanda taketa hidima kamar wasu bak'ine daban zasuzo basu libabatu ba.
      Wajen k'arfe d'aya da rabi uncle G! yatafi tarosu a tasha..............✍🏻





💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 21~November~2016



🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💞



🔶🔸5⃣2⃣🔸🔶

............Babu dad'ewa uncle G! yadawo d'aukeda su aunty hafsat, cikin matuk'ar fainciki sopy ta taresu, suma dai sunyi farin cikin ganinta, musamman ma Aysha.
    Sopy tacika musu gaba da kayan abinci, aunty hafsat ta ce, "o ni, k'anwata yaya zamuyi da wannan abinci haka, saikace masu cikin zani.
   Sopy tayi dariya tana fad'in duk nakune aunty, aii d'anyar fata bata fashewa.
  Sukayi dariya suna fad'in lallaikam, yau zamuci har mu kasa tashi, fareeda ta fito tana musu sannu da zuwa, suka amsa suna binta da kallo, dan basu santaba, ta zauna tana wasada Sayeed d'an gidan Libabatu.
    Uncle G! yafito, jikinsa sanye da farar shadda tas d'inkin nasa dai bodane kamar kullum, tayi masa matuk'ar k'yau,sai tashin k'amshi yakeyi, ya d'ora hula da farin gilas siriri.
   Aysha ta ce, "yaya ina zakaje, yad'an kalli bak'in agogon dake d'aure a tsin tsiyar hannunsa, ya ce, "Aysha xanje masallacine ko.
  Ta ce, "dan ALLAH zanje.
   Ya girgiza kai yana fad'in A'a bazanje dakeba, masallacin nan bakamar na gida bane.
   Sopy tafito daga kichin hannunta d'auke da tire, ganin uncle G! ya d'au kwalliya saita tsaya tana kallonsa.
   Ya kanne mata ido d'aya, tad'anyi murmushi tana nuna masa su aunty hafsat da idanu.
   Shima murmushi yayi tareda d'aga kafad'a alamu, so what, sopy ta ce, "uncle sai ina?, ya ce, "lallai kin manta yau juma'a?, ta ce, "o, masallaci fa ko??, ya jin jina mata kai yana lumshe idanu, ta ce, "to ALLAH ya tsare.
   Yad'an yima sayeed wasa yana fad'in amin sopyna, sayeed yashiga wangale baki yana mik'a masa hannu.
   Uncle G! ya d'aukeshi yana fad'in yaro masallaci zanje, yad'an yimasa wasa sannan yamaidashi wajen fareeda ya fice yana fad'in saina dawo.
   Sukace to adawo lafiya.

Yau kam sunasha hira abinsu, sopy tasha firar gurum, sun kawo masu tsaraba irinta k'yauye, tasu data gwaggo, babama ba'a barsa abayaba.
   Sai k'arfe hud'u uncle G! yadawo, sopy ta taroshi amma bakamar yanda ta sababa, saboda yau tana jin kunyar bak'i, ya zauna yana fad'in wash ALLAH!!; na.
   Su duka suka dawo da kallonsu gareshi,  Libabatu ta ce, "yaya ka gajine.
    Ya kwantar da kansa jikin kujera yana fad'in wlhy kuwa sosaima kuwa, sopy ta kawo masa ruwa, ya tashi yakarb'a yasha yana mata murmushi.
   Yagama sha ya mik'o mata kofin, ta karb'a tana fad'in abincifa uncle?, ya ce, "zanci dan wlhy ina jin yunwa.
   Sopy ta nufi kichin tana masa dariya, ta ce, "a ajiye a dinining ko akawo nan, ya mik'e yana fad'in kawo nan, sai naci muna hira, amma bari nafara watsa ruwa tukuna.
   Ta ce, to.
 Sunan zaune suna hira yafito sanye cikin k'ananun kaya, sopy takawo masa abinci, yanaci suna hira.
    Da magriba yatafi sallah, sukuma sukayi a gida.
   Saida akayi isha'i yadawo, yadawo musu da gasashshen tsire mai dad'i, sukaci suna farin ciki.
    Uncle G! ya ce, "oh, Safiyya namanta, albishirinki?, da sauri ta ce, "goro fari tas uncle.
  Ya ce, "to saiki kawomin goron sannan, sopy ta ce, "to mikake so?, yay shiru alamar tunani, can yad'ago yana mata wani irin kallo, wanda har yabata kunya, ta duk"ar da kai k'asa.
   Uncle G! ya ce, "alawar madara nakeso, ta yi d'an murmushi, dan ta fahimci inda yadosa, ta ce, "to kad'auka ka samu.
    Babu wanda ya fahimci inda zancensu yadosa, sai fareeda Dan haka ta had'e rai, tana jin haushi, azuciyarta ta ce, "jara babbu kawai,😜
  Ya murmusa, ya ce, "to, Asiya ta haihu d'azu, tasamu d'a namiji.
   Sopy ta k'an k'ame Aysha tana murna, ta ce, "uncle yaushe zamu?, ya ce, "to sarkin zumud'i aii k'ya bari sai gobe ko.
  Ta ce, "ALLAH yakaimu.
  Su aunty hafsat sukace amin.

Saida sukaga kowa ya kwanta sannan suka tafi d'akinsu suma, a d'aki uncle G! ya rungume sopy yana fad'in, yaufa ranar tadaban ce, ta d'ago tana kallonsa, ta ce, "miyasa yau tazama tadaban?.
    Ya murmusa, ya ce, "kedai zoki bani alawar madara, sopy ta rufe fuska tana fad'in kai uncle ALLAH karage abinda kakeyi, agaban su aunty kake fad'ar wata alawar madara.
   Ya ce, to aii basu ganeba ko?, ta ce, "aiiko sun gane, sundai yi shirune kawai.
   Ya jawota saman k'irjinsa yana fad'in, bawani ganewa dasukayi, saidai idan fareeda dan naga tanata b'ata rai.
    Sopy ta sumbaci k'irjinsa ta ce, "banida matsala da wannan.
   Uncle G! yayi dariya, ALLAH sopy ke muguwace, nakula kwanannan kin sako fareeda a gaba fa.
    Sopy ta ce, "niban sakata gababa, nagadai kawai rainin hankalinta yafara yawane.
   Nafito ina fad'in bari nad'an lek'o su fareeda suma, d'akin na tura ahankali nashiga, suduka sunyi barci, babu wani mai kwakwkwaran motsi, da sauri nafito, nadawo d'akinsu uncle G!, amma saidai kash harsun rufe d'aki, nadawo baya da haushi, dan naso naga miye alwar madarar da sopy zata bawa uncle G!, dan nima naje nabawa nawa mijin🙈😜................✍🏻





💞Bily💞
💞💞Mrs Abd[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 24~November~2016




🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💞



🔶🔸5⃣3⃣🔸🔶

..........Su aunty hafsat suna jin dad'in zama da sopy, to itamadai sopyn gareta hakane, tanajin a zuciyarta idan da haka dukkan dangin miji suke gsky da an zauna lfy a akasar hausa.
       "" dan kiyayyar dangin miji tana tasiri wajan ruguza tubalin ginin rayuwar aure, tana haddasa gaba da kiyayya nazumincin family guda biyu, yanasa 'ya'ya da tsanar dangin mahaifinsu, adalilin k'iyaya dasuke nunawa mahaifiyarsu, to ALLAH yasa mu gyara amin.""
      Uncle G! ya umarcesu da su shirya yakaisu suyi barka suduka, amma sai fareeda ta ce, "ita bazata jeba, zata zauna agida.
    Uncle G! ya ce, "yaza'a abarki agida ke kad'ai ai zaki takura, karki damu babu abinda zai faru sai alakairi, tunda suka fad'a da bakisu sun yafe miki.
   Fareeda dai tatsaya tsayin daka akan bazata jeba, haka suka hakura suka barta.
    Uncle G! yanaso yayi barci agidan, amma saboda gudin abinda zaije yadawo saiya hakura yafita.
    Su sopy suka shirya suka tafi, bayan ummy tazo tayi musu jagora.
    Da gudu sopy tashiga gidan tana kiran aunty Asiya, taje ta mamik'e katon jaririn da aunty Asiya ta haifa, wata sabuwar kaunarsa tana ratsata, jitake kamar itama tasamu k'ani ciki d'aya.
    Ummy tak'araso da su aunty hafsat cikin d'akin, aunty asiya ta ce, "ALLAH ya shiryaki sopy, shine kikayo gaba kika bar baki abaya.
    Libabatu ta ce, "ai bakomai tana murnane, anan suka wuni, akasha fira, su aunty hauwa'u ma sunzo, da zainab da Nafisa, aiko akasha hira kamar sun saba dasu aunty hafsat.
   Muna nan zune saiga gayyar 'yan professional writer  suma sun iso, sopy tayi matuk'ar farin cikin zuwansu,  tashige cikinsu anata shan hira da tambayar ina fareeda ta ce," musu tana gida suka barota.
    Sai wajen karfe biyar muka bar gidannan, bayan munci munsha daga mai k'yau, can na hango marakisiyya da madina sunata k'atuwar lauma, nayita harararsu dan karsu bamu kunya, amma ina saida sukaji sunyi nak, harda tambayar sopy wai kozasu sami wanda zasu kaima saratu ta fatima pii, dan karsu basu labari suji haushi akan su basu ciba.
    Da haushi ya isheni saina yo waje batareda najira amsar da sopy tabasuba😜😜.

     Agajiye suka shigo gida, sun tarar da fareefa a falo tana kallo, tayi musu sannu da zuwa, suka amsa suna zama, sopy ta ce, "fareeda uncle fa??.
    Saida ta yatsine baki sannan ta ce, "bai dawoba.
   Ko babu komai sopy taji matuk'ar dad'i da faruwar haka, dan dama bataso tabar fareeda da uncle G! agida d'aya su kad'ai, dukda tayi matuk'ar yarda da uncke G! d'in, amma tana tsoron sharrin shaid'an uban had'in tuggu, dakuma fareeda uwar gidansa, uwar cin amana.
    Agurguje sopy tayi wanka, tazo ta d'ora abinci, saboda kar uncle yadawo babu abinci agidan, kan kace mi gida ya kaureda kamshi mai dad'i, Libabatu taje kichin d'in tana tsokanar sopy, wai mitake dafa misu su manyan masu gida, sopy tayi dariya tana fad'in ai kune na robar, yanzu ina had'awa na k'arfenne, suka tuntsure da dariya harda tafawa kamar k'awaye, kai jama'a wannan zama yana burgeni, dangin miji kamar danginka.
     Sai gab da magriba uncle G! yashigo, agurguje yay wanka yanufi masallaci, sai bayan isha'i yashigo, sannan suma sunyi sallah, yashigo musu da kayan marmari, sukaci abinci suka k'oshi sannan aka shiga hira mai dad'i, saida sha d'aya tayi uncle G! ya ce, "bari suje su kwanta dan gobe sunada makaranta, badan angaji da hirarba kowa yaje ya kwanta.

Da safe da wuri sopy ta tashi tahad'a karin kumallo, suka shirya sukaci itada uncle G!, suka bar musu nasu, sukai musu sallama suka tafi, suma suka bisu da addu'ar dawowa lafiya.
        A maranta sopy tana tareda Nadiya, dan yau bataga zalihaba rediyo mai jini.
   Haka suka cigaba da karb'ar lectures har zuwa karfe shidda na yamma, uncle G! ya d'akkota suka dawo gida.
     Lafiyayyen abinci suka tarar su aunty hafsat sunyi, dan haka suna yin wanka sukaci abinci bayan sunyi salloli.

Haka rayuwa taci gaba da tafiya, kullum sopy sukan biya suga jariri kafin su tafi makaranta, takan had'a musu abincin safe ta gyara gidan kafin su tafi, sukuma suna yin na rana, saidai sopy ta lura fareeda bata aikin komai agidan sai su aunty hafsat, itadai saidai abata taci ta kwanta tayi barci, dan haka faridar tayi wani irin k'yau tak'ara farida kiba.
     Sopy bata tab'a tanbayarta miyasa bata aikiba, dan bata bukatar hakan.
    Da haka akasha sunan d'an gidan uncle kabeer, yaci sunan baban su sopy wato ibrahim, za'a rinka cemasa khalil, anrak'ashe an kwalle, ansha shagali, fareedama taje wajen sunan, saidai tanata rab'e2 saboda tsoron 'yan uwa saita saka nik'af, ba wanda ya ganeta saisu zainab, suma sai suka shareta sukayi kamar basu ganetaba.
     Mukan baruwanmu, danta shagalinmu mukeyi, uncle G! ma sun had'ama abokansu walima dai2 karfinsu, anzo antayasu murnar samu d'a.
     Sai wajen sha biyu suka koma gida, kowa yanemi makwanci ya kwanta saboda gajiya.
   Da safe da wuri sopy takoma gidan uncle kabeer ta taya kannan aunty asiya aiki suka gyara ko'ina tsaf.

Satinsu libabu biyu sukai haramar komawa gida saboda yara dasuka baro, uncle G! ya had'a musu shatar ta arzik'i suka tafi suna kewar sopy itama tana kewarsu, har kuka tayi konace sukayi, dan har auty hafsat saida ta matse hawaye, shikansa uncle G! yaji babu dad'i, dan zuwan 'yan uwansa ya k'ara masa farin ciki, saboda k'yaunar dayake musu, fareeda kanta saida tad'an matse hawaye saboda sabo, dahaka dai suka tafi suka barmu da kewa😭.

Yau tsawon kwanan su aysha biyu da tafiya, gida yakoma yanda yake, yau babu aiki dan haka sopy taje ganin masu jego, tabar uncle G! yana barci ad'akinsa, fareeda kuma tana falo.
    Fitar sopy babu dad'ewa zuciya tashiga zuga fareeda bisaga gurguwar shawara, har zuwa sha biyun rana bata gama aminta da shawarar zuciyartaba, saidai zuciyar tata taci gaba da karanta mata tafsir mai wuyar fassara, ta kalli agogo karfe sha biyu da kwata, tad'an murmusa tanada tabbacin ba yanzu sopy zata dawoba, tamik'e da suri tashiga wanka, tafito ta tsara kwalliya, mudai muna lab'e muna kallon ikon ALLAH, tagama tsaf tad'akko wata yololiyar rigar barci tasa ka, ta feshe jikinta da turare, d'akin uncle G! mukaga ta nufa, kunsan ALLAH nikaina 'yar rahotonku saida numfashina yaso ya d'auke, amma haka na lallab'a nabi bayanta.
     Ta shige d'akin tana ran gwad'a, ta maida k'ofa ta datse da key, tabi uncle G! dake kwance saman lafiyayyen gadonsa da kallo, dagashi sai gajeren wando yan barcinsa hankali kwance, dan yasha maganin mura.
    Fareeda ta k'awata fuskarta da murmushi tana wani sake gyara zaman rigarta, tabbas yau saita aiwatar da abunda tadad"e tana buru, koda sopy tayi nasarar hanata auren uncle G! tofa yau saitayi nasarar had'a makwanci da ita, dan babu makawa saita saka uncle G! ya bata ruwan dazai gusar mata da k'ishir warta.
     Ta taka ahankali harzuwa jikin gadon nasa, ahankali takai hannu zata tab'ashi kamar an ce yafarka, saiya tshi afirgice, cikin tsoro da fargaba yake kallon fareeda babu abunda yake ambata sai ""inna lillahi wa'inna ilairraji'un, "" wallahu galibun ala amrihi, wad'an nan sune addu'oi  in dasuke fita daga kan lab'b'ansa, fareeda kuwa tana gabansa tana wani jujjuya jiki da salo2 na yaudara, wanda shaid'aniyar zuciyarta take koyar da'ita.
    Adai2 wannan lokacinne kuma sopy tadawo, ta tab'a k'ofar taji arufe, bataso ta tadashi dan haka taje d'akinta ta d'akko wani key d'in, bata damu da rashin ganin fareedar ba, dan atunaninta tana kichin tana girki.
    Ji sukai ana bud'e k'ofa, cikin tsananin tsoro da firgici suka maida hankalinsu awajen, sopy ta bud'e k'ofar saidai tuni zuciyarta ta yi tsawa maikama da saukar aradu, ko kwaran kwatsa, binsu take kawai da idanu, dan kallo d'aya zakai musu kaga alamun rashin gsky atareda su............................✍🏻

Turkashi musu karatu, komai zai faru a wannan gida yau, lallai kila yau sai an kwatanta yak'in duniya nafarko awannan gida. Nima kaina a tsorace nake bare fareeda da uncle G!!!!!!!!!. 


Kuyi hak'uri darashin type na kwana biyu. 






💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 24~November~2016




🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷




NA BILKISA IBRAHIM💞



🔶🔸5⃣4⃣🔸🔶

...........Sopy tayi wani wawan tsale ta cakumi wuyan fareeda, wata muguwar shak'a tayi mata irinta mutuwa, idanun fareeda suka fiffito, tafara kakarin fitar rai, dan numfashinta sai safa da marwa yakeyi, uncle G! sai k'ok'arin b'an b'areta yakeyi amma yakasa, yarasa wane irin k'arfine da sopy.
     Ganin idan yay sakaci zata iya halaka yarin yar mutane, saiya saka k'arfi ya finciketa daga kan fareeda.
    Fareeda tafara murza wuya dan taji shak'a, sopy tak'ara kukan kura saman fareeda, kokawa ta kaure tsaka ninsu, dukda sopyce take jibgar fareeda wannan bai hana fareeda kare kantaba, uncle G! kuwa wajen k'ok'arin rabasu aka bashi naushi a baki, dole yay baya hannunsa rik'e da baki.
    Su sopy kuwa tuni sunkai falo, duk abinda kowa yasamu makawa d'an uwansa yakeyi, dan danan suka hargitse falon, babu abinda kakeji sai ihu da ashariyar da fareeda take kutun tumawa.
     Tabas fareeda tana shan duka, dan tun tana iya karewa harta fara gazawa, uncle G! ya d'auki waya yakira uncle kabeer, ya ce, "kabeer kataimakeni wlhy za'ayi kisa agidana, ka gaggauta zuwa, nakasa tab'uka komai saboda tashin hankali.
     Cikin rud'u uncle kabeer ya ce, "lfy? ??, kai dai kazo uncle G! yafad'a tareda kashe wayar yanufo falo.
    Fareeda ta rarumi wuk'a wai zata kashe sopy, uncle G! duk yarikice sai hak'uri yake bama fareeda.
   Amma sopy ko'a jikinta dan fuskarta bata nuna alamar tsoroba, sopy tad'auki filawa ta jefama fareeda jikake dauuuuuu agoshi, dan danan goshin fareeda ya fashe jini yafara ambaliya a fuskarta, dama duk anjimata ciwo a hannuwa da jiki.
    Fareeda tayi wata k'ara mai razanar wa, amma ko ajikin sopy, taje ta tad'e fareeda ta fad'i akan tayils takara fasa kai, da alama kafarta ta karye kokuma targad'e, hakan bai ishi sopy ba, ta hau kan ruwan cikin fareeda tacigaba da ribd'a, gaba d'aya hankalin uncle G! yatashi, gashi yakasa d'aga sopy daga saman fareeda, ga fareeda tanata kakarin mutuwa, da gudu uncle kabeer yak'aso, dak'yar suka iya d'aga sopy daga saman cikin fareeda.
    Sopy saijan ajiyar zuciya take kamar zata mutu, uncle kabeer yasan sopy idan tayi zuciya zata iya aikata komai, kuma tana samun k'arfi na musamman awannan lokacin, dan haka bai zargi uncle G! da sakakin hana sopy dukan fareeda ba.
    Ta kuma yun kurowa zata damki fareeda, unlce kabeer ya ce, "youseef kariketa, dan yanzu sopy bata cikin han kalinta.
      Ruk'o sosai uncle G! yayma sopy, amma sai fige2 takeyi tana fad'in ya saketa ta kashe fareeda kowama yahuta.
    Data kasa kufcewa saita fashe da kuka mai ban tasayi, acan kuma uncle kabeer yana k'ok'arin far fad'o da fareeda dan ta suma, tad'an dad'e kafin ta kawo numfashi, dak'ar uncle kabeer ya d'agata ya d'ora saman kujera.
    Kamar daga sama sukaji ana buga k"ofa, uncle kabeer yaje ya bud'e dan yasan ko su waye.

Suduka suka shigo, uncle G! yana binsu da kallo, akwai baban farida da mamarta sai k'anin babanta sai  yayyaenta maza biyu, sai zainab, sai baban sopy da inna saikuma aunty Nafisa da aunty hauwa'u da aunty asiya matar uncle kabeer, suduka kallon falon suke, dan kuwa ya hargitsu, lallai sun tabbata ansha gumurzu agidan.
     Suka kai dubansu akan fareeda dake kwance jina jina, sai kuma sopy da uncle G! yasaketa ganin iyayenta, yazata tahak'ura tunda taga iyayensu, amma ina baisan zuciyar sopy idan tab'aci akwai matsalaba.
     Yana sakinta kan fareeda tayi, tacigaba da jibga, baban tane ya wanka mata mari, wanda yasa tashiga hankalinta, ta zube a k'asa tana gunjin kuka, dan an hanata koyama fareeda darasi, mamar fareeda tazo ta rungume sopy tana lallashi, saida kowa ya natsa, aka zazzauna falon yayi ahiru, babu abinda kakeji sai shashshekar kukan sopy, wanan kuma sunsan bazata dainaba har sai ta huce, ko kuma an tofa addu'a acikin ruwa an bata tasha sannan.
    Wani mai kyamis dake bayansu uncle kabeer yakira, yazo yay musu diresin d'in wajajen dasukaji ciwo, na sopy kad'an ne, amma fareeda abin sai wanda yagani, ma gunguna yabasu sannan ya gice.
      Palon yay tsit kamar ruwa ya cinyesu, har tsawon minti goma babu wanda ya ce, "uffan.
     Sai can k'anin baban fareeda yay gyaran murya, tareda sallama suka amsa, ya ce, "yusufa miya kawo wannan d'anyen aikin a gidanka, kuma a ina kuka samo fareedatu???.
            Uncle G! ya sassauta murya cikin ladabi, yashiga basu labari tundaga zuwan fareeda gidan har zuwa abinda ya faru yau, baba yadawo kan fareeda ya ce,  "fareeda haka akayi, ta ce, "tunda taji uncle G! bai fad'i tsiyatakun datayiba, yadawo kan sopy wadda har yanzu tana ajiyar zuciya ya ce, "ke kuma mikika sani gameda hakan safiyya??.
    Sopy saitayi shiru, kowa yasan idan tayi zuciya batason magana, dan haka uncle G! yay saurin  ce wa, "a k'yaleta kawai wanda suka fad'a shida fareeda ya isa,  Dan baya so sopy  tab'aro komai.
      Baban fareeda  ya ce, "dolene itama tayi magana dan kar a tauyeta, uncle kabeer ya mika mata kofin ruwan addu'a takarb'a tasha, bayan "yan muntuna tadawo hayyacinta.
     Ta zauna ta zayyano duk abinda ya ke fatuwa tsaka ninta da fareeda, har abinda yasa Abdul ya koma kan fareeda, dan fareedar tafad'ama sopy komai da bakinta, tafad'i zuba mata gishiri da yaji da suga cikin abinci da fareeda tayi, har saka kayan barci tazo falo ta zauna saida sopy tafad'i, tafad'i gargadin data yima fareedar dan takiyayeta, dakuma abinda yafaru a yau.
    Sopy bata rage komaiba.
  Maman fareeda ta dakawa fareeda tsawa ta ce, "koki warware tuggun dakika kulla yau kokuma na tsine miki, nakuma kasheki da hannuna, yayanta ya zazzare mata idanu ya ce, "bazaki fad'aba muna fuka annamimiya.
    Fareeda dataga babu sarki sai ALLAH saita fad'i gskyr abinda yafaru yau, takuma wanke uncle G! daga zargi, danshi yak'i fad'ar komai.
    Uncle G! yaja ajiyar zuciya danjin ALLAH mai komai mai kowa ya kub'utsr dashi.
     Maman fareeda ta fashe da kuka danjin abinda d'iyar tata ta aikata, abin kunya da kazanta.
     Dak'ar aka lallasheta, ta ce, "kuma bazasu sake zama da fareedaba, saidai tanemi wasu iyayen badai suba.
     Nakula yau fareeda tayi nadama ta gsky, dan kallo d'aya zakai mata ka sheda hakan, kuka tashiga rerawa tana basu hakuri, da fadin tayi nadama walhy tayi nadamar aikata duk abinda yafaru abaya da yanzu, takumayi alkawarin canja halayenta.
    Baban ya daka mata tsawa ya ce, "makaryaciyar banza da wofi, ba haka kika cema su yufan ba yayinda ya tsuntoki, kekam inaga wutar ALLAH ce kawai zata sakaki nadama.
     Da sauri baban sopy ya karb'e da fad'in A'a bama fata, kuma ni na yarda da tubanta, dan haka zata koma gidana da zama, kafin ALLAH yabata miji tayi aure, sai dai ina nemar mata gafara daga gareku,, kuyi hakuri ku yafe mata, bakinku kawai zai iya hana dawwamar tubanta, zai kara jefata wajen aikata wani kuskuren, ku yafe mata dan ALLAH.
    da k'yar uncle G! da uncle kabeer da inna  suka saka baki, iyayen fareeda suka yafe mata, aka dawo kan 'yan uwa suma ansha fama kafin su yafe, sopy kuwa duk'ar dakai tayi dan baxata iya yafe waba, sunsan halinta sarai yanzu tana kan dokin zuciya, dan haka uncle kabeer ya ce, "su barta sai nan gaba, idan ta huce, dan ba'a tursasa mutum ya yafe zalincin da'akai masa.
    Haka aka hak'ura aka bar sopy, suka tusa k'eyar fareeda suka tafi, akabarsu aunty zainab suna gyara gidan sopy, dan yayi kaca2 kamar filin sukuwa.
    Gyara sosai sukai mata aka maida komai mazauninsa, wadanda suka fashe aka zubar, sai bayan isha'i suka tafi, bayan sun yimusu girki sunsaka sopy ta gasa jikinta da ruwa mai zafi, saboda tsamin jiki.

Suka tafi gidan shiru, dan uncle G! yana masallaci, tazuba abinci taci batareda tajirashiba, ta sha magani tashige d'akinta ta kwanta.
     Uncle G! ya dawo yaga bata falo saiya lek'a d'akinta, tana kwance akan gado amma da alama idanunta biyu, dan yaga tana karkad'a k'afafuwa, alamar har yanzu asama take, dazata samu wani dasaita ruburbud'a😜, kamar yanda ta suburbud'i fareeda😆😆😆👈🏻.
     Uncle G! yashigo jiki asanyaye, yak'araso kusa da gadon ya tsura mata idanu, kallo d'aya tayi masa ta kauda kai gefe, yad'an murmusa,  ya zauna kusada ita, yakamo hannunta dake saman ruwan cikinta, yad'an matsasu, tayi burus dashi, ya matso ya juyo da fuskarta gefen dayake, saita runtse idanu.
    Ahankali ya furta wai laifin mi nayi sopyna, idan nayi laifine sai asanar dani, wasu zafafan hawaye suka shiga zubowa daga kumatun sopy.
     Uncle G! ya jin jina kai, lallai ya yarda da batun uncle kabeer dayace fushin sopy bala'ine, shikam ya shaida yau,  yasa hannu yana share mata hawaye, ya dawo da kanta saman cin yarsa yana cigaba da lallashi, amma tak'i saurarensa.
    Dole yahakura yaje yaci abinci yay wanka, yayo shirin barci yazo yakwanta kusada ita, yay musu addua dan ita harma tayi barci.
     Shiko saiya kasa barcin dan abubuwan dasuka faru d'azune suka shiga dawo masa, gani yake kamar alabarin littafi ko film, ya dad'e bai barciba, saidaga baya ya saceshi shima. .............✍🏻 





💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's
[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 25~November~2016




🔷🔹NI DA AMINIYATA!!! 🔹🔷





NA BILKISA IBRAHIM💞




🔶🔸5⃣5⃣🔸🔶

...............Tsawon kwana uku kenan amma Sopy tak'i sakin jikinta, kwatata ta daina fara'a, bata shiga d'akin uncle G!, dan idan ta tuno da yanda tasamesu ad'akin shida fareeda sai taji hawaye na kwaranya a idaniyarta, lallai tana ji aranta da uncle G! da fareeda sunyi tarayya tofa da har abada ta barmata uncle G!😳.
     Gaba d'aya uncle G! yarasa kanta, tun yana lallashi har yabari dan yafara jin haushinta shima, yayi fushinsa na kwana d'aya ya sakko dan dole yakoma lallashinta.
     Yauma tana zaune afalo ita kad'ai ta kurama tv ido,saidai azahiri ba kallon takeyiba tana duniyar tunanine, uncle G! yashigo hannunsa nik'i2 da kaya, kwata2 sopy batasan ya shigoba, dan tunaninta baya tareda duniyarta.
   Ya dire kayan a tsakkiyar falon, ya nufo gareta, ahankali ya zauna kusada ita, yajawota zuwa jikinsa, tai figigit alamar dawowa, cikin d'an rikicewa ta ce, "sannu dazuwa, ALLAH bansan ka dawoba.
    Uncle G! yay d'an murmushi tareda shafa gashinta ya ce, "yaza'ayi kisan nashigo bayan kina duniyar tunani, ya kuma mayseta ajikinsa yana fad'in sopyna plz yakamata komai ya wuce, ki d'ebi abinda yafaru ki watsashi baya, muci haba da gina sabuwar rayuwa, ki d'auki hakan a matsayin k'addararki ta rayuwa.
    Sopy ta zubo da hawaye tak'ara kwanciya luf ajinkin uncle G!, shikuma yana shafata kamar mage, ta ce, "nakan dad'e ban damu da abuba koda yafaru a garenine, amma daga lokacin da'aka kaini mak'ura nakan shiga rud'ani da gushewar farin ciki, tad'ago tana kallon fuskar sa, ta ce, "uncle!! plz ka kaini wajen dazanyi kamar sati biyu, wannan ce kad'ai mafitar dazata mantar dani, rud'anin danake ciki a yanzu.
    Uncle G! yay murmushi ya ce, "indai hakan zai sakaki farin ciki tofa zan miki, dama na shirya mana tafiya Gurum tunda makarantarmu mun shiga yajin aiki,  tad'ago da sauri tana kallonsa tai saurin fad'in dgsk??.
   Ya jin jina kai alamar eh.
  Ta ce, "amma baka fad'a mini ba.
  Yashafa kanta ya ce, "naga kina cikin rud'anine", yad'ora da fad'in idan kuma bak'ya son Gurum toki fad'i inda kike so sai muje, domin samun farincikin ki.
    ta murmusa tareda murza tafin hannunsa, tad'ago tana kallon k'yak'yk'yawar fuskarsa ta ce, "aii nafison Gurum fiye da ko ina.
     Shima murmusawa yayi ya ce, "ngd da k'aunar dakikema garina.
   Tad'an harareshi oh, garinka mane kai kad'ai?.
   Yay 'yar dariya ya ce, "sorry garinmu.
    Yaudai babu laifi sund'anyi hira, har aka ci soyayya a wajen barci.
   Na girgiza kai ina fad'in mata da miji sai ALLAH.

 Bayan kwana biyu suka shirya, zuwa Gurum, babu yanda baiyi da'itaba akan suje su gaida su inna ba, amma ta ce, "bazata jeba, har k'ararta yakai wajen uncle kabeer.
    Uncle kabeer ya ce, "ya k'yaleta, yasan saboda fareeda ta ce, "baza tajeba", kuma hakan yayi, inko taje tofa sabon fad'a zai tashine.
    Uncle G ya ce, "haba aii ta hak'ura, uncle Kabeer yay dariya ya ce, "lallai nakula har yanzu bakasan halin sopy ba, ta hakura ne dan bata ganinta, amma sopy tafi kurma naci awajen fad'a.
   Uncle G! yay dariya yana f'ad'in ga k'arfin tsiya, dariya sukayi suduka suka kashe wayar uncle kabeer yana fad'in nidai babu ruwana, kunfi kusa,  .

   Yaukam tunda safe Gurum tai d'iba, shabiyu a Gurum tayi musu, su gwaggo sunyi farin cikin ganinsu, anmusu tarba mai k'yau, abinci har sopy ta rasa wanda zata ci.
    Aysha ta gyara musu b'an garensu.
    Da yamma baba yadawo daga gona shima yayi matuk'ar farin cikin ganinsu, yay musu godiyar hidimar dasuka sha da su Libabatu, yasa musu albarka sosai, itadai sopy saijin kunya takeyi.
     To haka rayuwa tacigaba da tafiya mai tarin farinciki, dan Gurum tayi musu dad'i, gashi kullum sai aysha ta raka sopy gidajen 'yan uwa da abokan arzik'i, tun uncle G! yana nuna baya so har ya hak'ura.
     Yau kwanansu hud'u da zuwa, sopy ta yashi da matsanancin zazzab'i, tun dare take zuba amai, har zuwa safiya, duk jikinta yasaki, saida safe uncle G! ya sanar da su gwaggo.
     Cikin hanzari gwaggo tazo b'an garensu, ta iske sopy tanata shek'a amai, ta kalli uncle G! ta ce, "yusufa yakamata kakira mas'ud abokinka yazo ya dubata ko?.
     Uncle G! ya ce, "to gwaggo, bari naje naga idan yana nan, gwaggo ta ce, "to ALLAH yasa adace.
   Ya fice yana fad'in amin, babu dad'ewa suka dawo tareda mas'ud shima d'an Gurum ne, tare sukai piramary da secondary, ya duba sopy sosai, saiya saka mata k'arin ruwa yatafi dan ya bincika abinda ke damunta.
     Karin ruwan da aka saka mata yasatayi barci, gwaggo da uncle G! zaune sun saka sopy Gaba sun zabga tagumi, baba kuma yana daga k'ofar d'aki zaune akan dankari, shimadai yayi shirun, aysha kuwa ta garzaya domin sanar da su aunty hafsat halin da'ake ciki.
    Sai wajen karfe d'aya mas'ud yadawo, sannan su gwaggo sun fito, ya mik'ama uncle G! hannu yana murmushi.
    Jiki a sanyaye uncle G! yabashi sukayi musabaha, mas'ud ya ce, "my Brother congratulation on your success!".
    Cikin rashin fahimta uncle G! yake kallonsa, ya daure ya ce, "d'an uwa ni wane arzik'i nasamu da har zaka tayani murna.
   Mas'ud yay murmushi ya ce, "kasamu babban arzik'i wanda wasu da yawa suke nema, harma dani aciki,kasamu k'yauta wadda ALLAH kad'aine yake badawa,kasamu arzik'i mai tarin ni'ima, na samun d'a daga matarka Safiyya!.
    Cikin matuk'ar farin ciki ya rungume mas'ud, yana fad'in "Alhmdllhi ALA kulli halin", lallai nayi maraba da samun wannan d'ingimemiyar k'yauta, ina kuma godiya ga sarkin sarakuna, mai so dak'aunar bayinsa.
   Uncle G! Yadawo da kallonsa ga sopy yana murmushi, lallai ALLAH yasoshi daba'a zubarmasa da d'a ba  wajen dambe.
   Sun dad'e suna murna kafin gwaggo ta shigo, itama mas'ud ya fad'a mata, dan uncle G! yakasa saboda kunya.
    Dan danan gida ya kaure da murna, harsu aunty hafsat ma sunzo tun d'azu, kowa farin ciki yake zasuga d'an uncle G! Aduniya, gwaggo da baba jisuke kamar yau suka fara samun jika, bare kuma uban ginsami uncle G!, aii jiyake yafi kowa sa'a a wannan rana.
    ""wannan na sopy ne da uncle G!!!!👍🏻😘😘👌🏻"".......................✍🏻






💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 26~November~2016





🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷




NA BILKISA IBRAHIM💞




🔶🔸5⃣6⃣🔸🔶

.............Sopy bata farkaba sai la'asar bayan ruwan da'aka saka mata ya k'are, uncle G! ya taimaka mata tayi wanka dan taji k'arfin jikinta.
     Su aunty hafsat suka shigo suna mata sannu, gwaggo takawo mata Abinci da Awara da fura wadda tasha nono mai k"yau.
     Aunty hafsat ta ce, "k'anwata azuba miki abincin ko? kici.
   Sopy tad'an yatsine fuska ta ce, "aunty nak'oshi, uncle G! ya harareta ya ce, "mikike nufi da kin k'oshi, haka kikeso ki zauna da yunwa?, tun jiyafa rabonki da cin abinci.
    Gwaggo ta ce, "A'a yusufa abita ahankali, gwaggo ta matso kusada ita, ta ce, "d'iyata daure kici koda awararce, ko fura, fad'a min wanne kikeso, inkuma bak'ya sonsu a sake miki wasu.
     Sopy ta ce, A'a Gwaggo zanci awarar, to shikenan gwaggo ta fad'a, Libabatu ta zuba mata awarar ta mik'a ma uncle G! dake kusada ita.
    Ya d'auka yakai bakin sopy, sopy tayi k'asa da kai dan kunya, ahankali ta furta uncle kabarsa zan iya ci dakaina.
     Ya ce, "karb'a kici kinga hannunki akwai datti gashi kuma jikinki babu k'arfi.
     Gwaggo dake jinsu ta ce, "in bata son naka, bari ni nabata, da sauri sopy ta bud'e baki uncke G! ya saka mata awarar.
     Abun yabasu dariya, dan haka suka tuntsure da dariya suduka d'akin, aunty hafsat ta ce, "k'anwata kunyarki tayi yawa.
     Gwaggo ta ce, "aii haka akeson mace takasance mai kunya, Dan kunya adon mace .
   Sopy tad'anci Awarar, dan tayi mata dad'i sosai, bayan tagama ta k'ara kwanciya, uncke G! ya ce, "tashi kid'an zauna ki huta, kar kwanciyar tayi yawa.
     Gwaggo ta ce, "A'a kabarta ta kwanta, k'ila tafi jin dad'in kwan ciyar.
    Ya ce, "to.

Sai dare su aunty hafsat suka tafi.
    Baba ya sissiyoma sopy abubuwan kwad'ayi ya ce, "abata taci, bayan yai mata sannu suka tafi b'an garensu.
    Uncle G! ya kalleta yana murmushi, ya ce, "lallai ke 'yar gata ce, kowa jiyake dake, tayi murmushi tana fad'in kokana kishine?.
     Ya murmusa tareda d'ora hannunsa akan cikinta, ya ce, "bawani kishi, kema aii gamasu kwace miki fada nan sun kusa zuwa.
    Cikin rashin fahimta sopy ta ke kallonsa, ta daure ta ce, "ban gane abinda kake nufiba??, ya kanne mata ido d'aya ya ce, "zaki gane, alokacin da yarona ko yarinya suka fara aikin 'yan kwallo acikinki.
    Sopy ta zaro idanu waje ta ce, "kamar ya ya?, ya kwanto da kanta bisa cinyarsa, yad'ora hannunsa saman cikinta, d'ayan hannunsa yana shafa gashin kanta, ya ce, "Inada babbar ajiya awannan cikin, ma'ana saka makon ciyonki na bayyanar yarona ne.
     Sopy tasaka hannu ta rufe fuska dan tagane miyake nufi, yay 'yar dariya, lallai yarinya kardai kice yarona d'an farin k'auye za'a maidashi?, to wlhy ban yardaba, garama tun yanzu na fad'a miki, dan banyarda a b'oyema yarinyata ko yarona suna ba, banyarda atureshi saboda yazo a matsayin d'an fariba, yasa hannu ya cire hannunta data rufe fuska dashi.
      Saita rintse idanuwa, yakai bakinsa kan nata, yafara al'amura.
   Na ce, "hummmm shidai uncle G! baya gajiya dayin kiss, bare kwana biyu ba'a had'uba.

Haka al'amura suka cigaba da tafiya a gurum, sopy tana shan tarairaya, duk abinda ta ce, "tana so sai an nemamata, koda awajen gurum yake kuwa, gwaggo ta hanata aikin komai, d'akinsuma Aysha ce take gyarawa kullum, a b'an garen uncle G! kuwa abin ba'a magana, suma su lubabatu suna bada gudummawa, dahaka sati biyun dasuka d'ebo tacika.
      Amma baba da gwaggo sun hana tafiya, sunce tunda ba'a koma makarantar ba to bazasu tafiba sai sopy ta k'ara samun sauk'i, badan uncle G! yasoba dole ya hak'ura.
     Shikam yana so su tafine dan yana cikin takura, gashi kuma wata sa'inma sopy a d'akin gwaggo take kwana idan jikin yay tsanani, itama kanta sopyn ya lura yanzu gudunshi takeyi.
    Itako sopy bataso uncle G! yazo mata da buk'ata ne, shiyyasa take baya2 dashi, dan bata so yacika takura mata.
    Kunsan wani cikin yana faruwa haka.

In tak'aice mu dai saida sukayi wata d'aya dawasu kwanaki, dan saida aka sanar an koma yajin aiki sannan baba yabarsu suka dawo kano.
     Sun dawo cike da kewar muta nen gurum, yayinda suma suka barosu da kewarsu.
     Tsaf suka tarar da gidansu an gyara, wananan duk aikin aunty Asiyane, sunji dad'i sosai, suna zuwa sai wanka da cin abincin da aunty asiyar ta aiko musu.
    Bayan sun gana suka kwanta dan su huta.

A b'an garen fareeda kuwa al'amira sai ahan kali, dan ba komai take nema ta samuba, sauk'in tama tana agidan su sopyne, amma tayi bak'i ta rame kamar ba'itaba,  kullum sai inna ta ce, "taje ta gaidasu mama.
    Badan tasoba take zuwa, dan idan taje gidan sai mama ta had'e mata rai, daga ita har baba basa sakar mata fuska, lamuran suna damunta, amma tasan laifintane.
    Yau ma tana zaune ad'akin sopy nada, ta had'a kai da guywa, hawaye suna kwaranya a idanunta, tana tuna rayuwa irin ta gidan sopy, duk da uncle G! bamai kud'i bane, amma yana k'ok'ari akan iyalinsa, yana wadatasu da cima mai dad'i, amma nan daga tuwo sai shinkafa, tarik'e kai tana hawaye.
    Araina ne ce, "su fareeda anji jiki, an shiryu badan ALLAH ba😜.....................✍🏻





💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 27~November~2016





🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷




NA BILKISA IBRAHIM💞 



🔶🔸5⃣7⃣🔸🔶


BAYAN WATA TAKWAS
...........Rayuwa mai gudu da sauri, daga safiya tayi sai gari ya waye, fareeda dai an shiryu da gsk, dan takoma makarantar islamiyya, gashi takoma wata shiru2, batada burin daya yuce tasamu miji tayi aure itama ta zauna agidanta, kullum kuma tana cikin yin istigifari, takan shiga gidansu ta taya mama aiki, dukda har yanzu mama bata sakar mata fuska, haka aikin inna duk ita takeyi, damuwar ta d'aya sopy, dan har yanzu sopy bata yafe mataba, ko gidan tazo bata kulata, gaisuwama sama2 sukeyi, kullum burinta ALLAH yakawo randa sopy zata yafe mata sukoma yanda suke da.
    Inna tana k'ok'ari wajen yiwa sopy nasiha akan tayafema fareeda tunda ta shiyu, duk sanda tazo gidan saita yimata irin wannan nasihar.
    To itama sopyn tayarda fareeda ta canja, amma tanaso tak'ara shiryuwane kafin ta ce,  " ta yafe mata, dan tuni ta yafema fareedar batadai furta bane kawai.   

GIDAN SOPY
Sopy anata fama da k'aton ciki, wanda da'alama ranar haihuwa kawai ake jira, dan tama daina zuwa makaranta.
    Afalo na isketa itada uncle G!, tana zaune a saman kafet ta mimmik'e kafafuwa, tasaka filet d'in kankana a tsakkiya tana sha, uncle G! Yana gefenta kwance a doguwar kujera.
    Ya kalleta ya tuntsure da dariya, sopy tajuyo tana kallonsa, ta ce, "miya baka dariya? hubbina!.
   Cikin dariya uncle G! Ya ce, "wlhy ke kika bani dariya sopyna, jibi yanda kika mik'e kafafu kina shan kankana, ALLAH kirage ci, nakula aranafa saikici abinci sau biyar.
    Sopy ta murgud'a baki😏 tana fad'in to waye yaja mini?, aii dai kowa yasan da bahaka nake da ci kamar jakaba ko?.
    Uncle G! Ya kwashe da dariya, ya ce, "aina kusa kad'a miki tanbarin acici kazar gona.
   Sopy ta watsa masa harara, saikuma ta shagwab'e fuska tafara kukan shagwab'a, ya sakko yana gintse dariya, kusada ita ya zauna yana shafa bayanta ahankali, acikin kunnenta ya ce, "yakamata kibar shagwab'a, dan kinkusa zama momy.
    Yasa hannu ya share mata hawayen fuskarta.
  Ta ce, "to ba kaibane kake tsokanata, ya sumbaci kuma tunta yana fad'in to yi hakuri na bari maman baby.
   Yanzu mikikeso nayi miki danki huce, ta nuna masa k'afafunta da sukayi d'an fushi.
   Yay murmushi dan yasan mitake nufi, ahankali yafara mammatsa mata kafafun, ita kuma tafara lumshe idanu, ya ce, "karfa kiyi mini barci 'yammata!!.
     Sopy tad'an bud'e idanu tana murmushi, ta ce, "kasan kuwa harna fara jin barcin wlhy.
    Ya ce, "aii ke yanzu kin zama kasa, dan ko fira bak'ya barinmu muyi, b'urun2 saikice aje akwanta, ta ce, "to yazanyi hubbina!, nima ba laifina bane, ya ce, "gsky ne laifin babynane, yafad'a yana kanne mata ido d'aya.
     Ta ce, "yauwa hubbina wai yaushe kacema Aysha zata zo?, ya ce, "sai ranar juma'a, tunda ta ce, "Al'hamis za'ayi musu hutu.
    Sopy ta ce, "ALLAH ya kaimu, yakuma kawo mana ita lfy.
  "Amin uncle G! Yafad'a yana murmushi.

🔹🔹🔹🔹🔹🔹🔹
   Yau dawuri uncle G! yafita dan zaiyi lectures d'in safe.
    Sopy ta tashi tad'an gyara gidan iya inda zata iya, dan yau bata jin dad'in jikinta kwata2, tana dai daurewane dan bataso tahana uncle G! fita aiki, tad'an cije leb'e ta rik'e bayanta da hannu d'aya, tadafe kujera da d'ayan.
    Tad'an dad'e tsaye tana shan azabar ciyo, daga bisani yalafa, ta rarrafa dak'yar takoma bedroom.
    Tana zuwa tazube agado, tanata murkususu, saidaga baya wani bacci mai dad'i ya saceta.
                Agigice ta farka domin jin wani azababben ciyo, mai kamada na fitar rai, ai bata san sanda ta silmiyo daga gadoba, babu abinda takeyi sai salati da kiran sunan ALLAH, dak'yar ta iya d'aukar wayarta, batare da tasan nomber ko wayeba takira kawai, ALLAH yasota aunty Asiya takira, dak'yar ta ce, "plz kowaye yazo ya taimakeni zan mutu.
    Aunty asiya bata jira ta karasa ba, ta fito da sauri daga gida, gidansu ummy ta mik'a khalil, agurguje tazo gidan, sanda ta iso sopy harta fita hayyacinta, dan kuwa haihuwa ce gadan2.
    Aunty asiya ta rik'eta tana mata sannu.
    Ita dai sopy babu abinda takeyi sai ambatar sunan ALLAH, da duk addu'ar datazo bakinta, zuwa can tasaki wani uban nishi, jikake wani kacam, d'a yafad'o, yana tsanyara ihu.
   Aunty Asiya ta ce, "masha ALLAH, sopy sannu da aiki.
   Aunty asiya takira ummy ta ce, "ta turo mata mamarsu.
   Babu dad'ewa mamarsu ummy tazo, aka yanke cibiya, tareda d'auke sargad'ed'iyar yarinya maikama da babanta, maman ummy ta ce, "masha ALLAHU, da zuwan wannan k'yak'yk'awar yarinya duniya gidan gwa gwarmaya.................✍🏻






💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞

27~November~2016




🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷



NA BILKISA IBRAHIM💞



🔶🔸5⃣8⃣🔸🔶

...........tsaf suka gyara jaririya da sopy, Aunty Asiya takira uncle kabeer ta sanar masa, shikuma yasanar da uncle G!, dan danan labari ya karad'e dangi, har muta nen Gurum labari yakai musu, acanma murna ce ta kaure, da addu'oin fatan alkairi ga jaririya, bak'uwar duniya.
        Uncle G! ya iso cikin murnarsa, bai damu da makwaftan dasuke zaune afaloba, suka gaidashi tareda yimasa barka.
      D'akin sopy ya isa cikin matuk'ar zumud'in son ganin jaririyarsa, yana shiga ya rungume sopy dake bakin gado tana shafa mai, dan batajin ciwon komai, saidai aunty asiya ta ce, "ta shirya suje asibiti aduba lafiyarta itada baby.
    Sopy tad'ago tana kallonsa, suka sakarwa juna murmushi, ya ce, "sannu sopyna, ya jikinki??, sopy ta ce, "komai nomal hubbina.
    Ya ce, "masha ALLAH, aunty asiya tashigo da sallama, suka amsa, ta mik'a masa jaririyar da'aka shirya cikin fararen kayan sanyi masu laushi.
    Yasa hannu biyu yakarb'a, ya tsura ma  jaririyar ido kamar zai cinyeta, yad'an mannata da jikinsa tareda lumshe idanu yana zubar da hawayen farinciki.
     Sopy tasaka hannu tana share masa, yad'an dad'e ahaka sannan ya bud'e idanu, ya sauke akan jaririyarsa, mai tsananin kama dashi, tanata barcin ta. 
    Tad'an motsa kad'an, yay saurin fad'in sorry my dear, yad'an jijjigata kad'an, takoma barcinta.
    Sopy ta ce, "hubbina santin baby ya hanaka magana ko??, yad'ago yana murmushi, ya ce, "sopyna k'yautar d'a!! dabance, bazan iya misalta miki irin farincikin danake cikiba yau wlhy.
     Sopy ta ce, "aii naga alama, dadyn baby!!.
    Uncle G! ya ce, "haka zancen yake, amma zonabaki sunan babyna, sopy ta mik'ama uncle G! kunnenta, ya gwargwad'a mata, tayi wani murmushi tana fad'in inko haka ta kasance to kayi halacci hubbina!.
    Ya ce, "ko? Sopyna!.
     Ta ce, "ALLAH kuwa.
Ya ce, "anyi an gama, barima kiga nayi maya hud'uba.
    Uncle G! yay mata hud'uba sannan suka tafi asibiti dan aduba lafiyarsu.
    Haka akayita hidima, koda yaushe gida cike da 'yan barka, su aunty Nafisa kuwa kullum sai sunzo, fareedama tazo saidai sopy bata sakar mata fuskaba sosai, itako fareeda bata damuba tanata rungume jaririya danji take wata irin k'aunar yarinyar tana shigarta.

   Yau muta nen gurum sukazo mota guda, aka had'a musu cima masu dad'i, sukaci sunata santi, sai yamma suka tafi akabar su aunty hafsat da libabatu da aysha anan, komai yana tafiya yanda akeson gwaggo ta had'o ma sopy kayan barka sosai, mutane sunata santi kayan, dan gwaggo ta taka rawar gani.
    Yau kuma aka kawo naman k'auri daga gidansu sopy, suma sunyi k'ok'ari, dan d'an akuya guda uncle kabeer ya siyo aka gyara, suma sunyi rawar gani wajen had'o kayan barka, ayau kuma shima uncle G! ya kawo nasa kayan barkar, abindai sai wanda yagani, komai dai2 saidai mak'yi zai kushe.

RANAR SUNA.
  yaune akasha sunan baby wadda taci sunan BILKISU MAI GADON ZINARI", lallai uncle G! yay mini halacci kuma nagode.
    Bayyana muku yanda taron suna yakasance b'ata lokacine saidai fa, ansha shagali na ban mamaki, groups dayawa sun halacci taron sunan baby Bilkisu!, irinsu.👇🏻
💞PROFESSIONAL WRITER
💞ZUMUNTA GROUP 
💞HAUSA NOVELS
💞 MANSHAT NOVELS
💞PRECIOUS WRITER' FORUM
💞IKKIAM'S NOVELS
💞HAUSE OF NOVELS
💞SO DA K'AUNA GROUP 
💞FASHION & NOVELS
💞BEST FRIEND'S 
💞LABARUN LITTATAFAI
💞HAUSA NOVEL BOOKS
💞 MACE MUTUM GROUP, ma sun halacci wannan taron suna, harma da groups d'in daban fad'aba, suyi hak'uri amma suma duk mun gansu.
     Dahaka taron suna yatashi lafiya, akabar  mai jego da jaririya Bilkisa, tareda dadynta uncle G!!!.
    An kawo musu tsohuwar dazata kula dasu, har suyi arba'in, AYSHA ma ta nan anbarta, saboda wasu ayyukan.

Bayan arba'in, baby Bilkisu tayi b'ul2 da'ita gwanin sha'awa, tana shan tarairayar iyayenta, dan uncle G! yana dawowa aiki zai d"auketa sallah ce kawai takesawa ya ajiyeta, ranar weekend kuwa ai ahannunsa take wuni, yayta mata wasa tana b'angale baki, sunje Gurum yawon arba'in, an kaiwa gwaggo da baba sunga jikarsu, takosha addu'oi, awajen kakanninta.
    Ananma kano sun zagaya gidajen 'yan uwa da abokan arzik'i, daga baya sopy ta tattara takoma makaranta itama..................✍🏻



WASA KWAKWALWA.
     wannan sak'one daga gareni, inaso ku fad'i abinda yake ranku game da wannan littafi mai suna NI DA AMINIYATA!!!.
      SHIN WA👇🏻
☆WAKUKAFI TAUSAYI??.
☆WAKUKAFI JIN HAUSHI??.
☆WAKUKAFI SO???.
☆ WAYAFI BIRGEKU??.
        Karki bari ayi babu ke, fad'i ra'ayinki, ko gyara gareni agun danayi kuskure.
   Idan kuntashi, kusaka sunanku, da gruop d'in dakuke, dakuma ra'ayinku.
   Inanan ina jiran sak'wanninku, ta hanyar gruop gruop d'inku, dan saikun rubuta ra'ayoyinku kafin mu kalmashe bakin wannan labari, daga nan zuwa ranar litinin.
    Plz karkuyi sanya, nagode sosai da k'yaunarku gareni.
   SAINA JIKU📢📢📢📢!!!!!!!!!!!!!.





💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞

[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 28~November~2016





🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷




NA BILKISA IBRAHIM💞



🔶🔸5⃣9⃣&6⃣0⃣🔸🔶

.............haka rayuwa tacigaba da tafiya, su sopy suna rainon baby bilkisu, yanzu haka tafara zama, uncle yadawo da Aysha wajensa, an nema mata makaranta tana yi anan, haka sopy tana zuwa makaranta kuma tana fahimta, abunda bata ganeba uncle G! yana nuna mata.
     Adai2 wannan lokacinne kuma aka sha bikin fareeda da wani d'an anguwarsu salmanu, yanada mata d'aya da yara uku, fareeda ta aureshine kawai amma badan yayi mataba, dole ta aureshi dan zaman gidan ya isheta, gasu baba sun dameta akan tafito da miji, to hakadai aka rurrumata aka kaita, indama ALLAH yasota ba gidansu d'aya da kishiyarta ba, gidan hayane d'aki d'aya ya kama mata, suna had'akar bayi da kichin da sauran 'yan hayar gidan, bawata cimar arzik'i, shinkaface fara da mai da rana da safe kuwa koko da k'osai shima idan kin samu, da daddare tuwo, dan haka fareeda duk tafita hayya cinta ga wani uban bak'i datayi kamar ba itaba, shiyyasa kullum cikin kuka take da nadamar abinda ta aikata abaya, ALLAH yasotama sopy tayafe mata harda uncle G!.
       Agidan sopy kuwa abun su d'anas komai yana tafiya yanda suke so, ga mijinta yana nuna mata soyayya mai tsafta, koda yaushe k'ara tattalinta yake, itama k'ara sonshi take kullum, ga 'yar d'iyarsu abin sha'awa da burgewa.
     Aunty asiyama ta sake haihuwar mace, itama suna cin soyayyarsu da uncle kabeer, komai yana tafiya musu dai2.
     Haka yayun sopy sumadai Alhmdllh, komai dai2.
    Mutan gurum ma a b'angarensu komai nomal masha ALLAH.


BAYAN SHEKARA TAKWAS.
       Nayi shiri nida 'yan kazagina su madina, gidan uncle G muka nufa dan mu gano muku halin da suke ciki, tun a tsakar gida nafara gamo da yara biyu duk maza, 'yan kimanin shekara 6, d'aya ya ce, "mas'ud mima momy ta ce, "mukarb'o mata?.
     Ya ce, "kaji mus'ab d'innan bakai ta gaya mawaba, zaka wani tambayeni?.
   Mas'ud ya ce, "to mukoma mu tambayo?, tafd'i mus'ab yafad'a yana kallon mas'ud, ya ce, "wlhy bazan komaba kana ganin aunty bilkisu tana nemana ta daka saboda na d'aukar mata sweet d'azu, idan zakaje  keje ina nan ina jiranka, dan baxan shiga cikin gidaba harsai dady yadawo.
     Madina ta kalleni ta ce, "da'alam yarannan fa yaran sopy ne, bakiga kamabane??, na ce, "nagani madee kuma inaga tagwaye ne.
     Ana cikin haka saiga uncle G! Yadawo, dagu su mas'ud sukaje suka rungumeshi, shima yataresu da murna, d'ai2 ya d'aukesu yana d'agawa, ya ce, "yaran dady sai ina??.
     Mus'ab ya ce, "momy ce ta aikenmu kuma mun manta, uncle G ya ce, "to kumuje ciki.
    Mus'ab ya ce, "dady ALLAH aunty bilkisu zata dakeni, uncle G ya ce, "kamata laifine ko??, mas'ud yay saurin fad'in dady sweet ya d'aukar mata, uncle G ya ce, "lallai kayima aunty bily babbab laifi, yafad'a yana jan hannunsu.
     Muka gaidashi muma, sai asannan ya gammu, cikin murmushi ya ce, "lallai yau munada babbar bak'uwa, bily kece agidanmu?.
    Nayi dariya na ce, "nice uncle G!, kuna nan lafiya?, ya ce, "lafiya k'alau muke, kushiga mana, aii sopyn tana ciki, mukace to.
     A falo muka tarar da bilkisu rik'e da wata 'yar k'yak'yk'yawar yarinya, wadda zata kai shekara d'aya.
    Bilkisu tazo ta rungume dadynta, yashafa kanta yana fad'in aunty bily ga takwararki, ta ce, "dady wace takwarata??, ya nuna mata ni, da sauri tazo ta rungumeni tana gaisheni, naja hannunta muka zauna saman kujera, su madinama suka zauna.
     Uncle G! Yad'auki karamar yana fad'in little sopy ykk??, yarinya ta shiga tsalle tana dariya da alam tasan dadynta,   ya ce, "aunty bily jeki kira momy kice tayi bak'i.
    Bily ta ce, " to dady.

Babu dad'ewa suka fito tareda sopy, sopy ta zaro ido dan mamaki, ta ce, "bily kece yau agidanmu, dama baki manta damuba??.
    Nayi dariya ina fad'in yazan manta daku, abubuwane kawai sukayimin yawa.
   Sopy tayi dariya tana fad'in lallai dadyn bily yau kayi mana babban kamu, aina kasamo mana bily??.
   Ya ce, "wlhy anan na had'u da'isu a tsakar gida.
   Sopy ta ce, "lallai kam sannunku dazuwa, mukace yauwa, dan danan aka cika mana gaba da kayan ciye2, aka shiga firar yaushe gamo, ananma nakejin fareeda ta haihu harma gobe suna, na ce, "yaranta nawa yanzu, sopy ta ce d'ayace mai sunana safiyya saikuma yanzu ta haifi namiji.
     Nace ALLAH sarki ALLAH yaraya, kema ai naga kun had'a family keda uncle G!, sukayi dariya, uncle G ya ce, "hud'une kawai, bilkisu takwararki sai 'yan biyu mus'ab da mas'ud sai auta safiyya k'arama.
    Na ce, "masha ALLAH, ALLAH ya raya mana su.
  Suka ce amin.
   Sopy ta ce, "mus'ab ina aiken dana yimuku??, mas'ud ya ce, "momy mun manta shine muka dawo danmu tanbaya.
    Sopy ta dafe kai tana fad'in naga takaina, waiku wad'anne irin mashiriritane, aunty bily tashi kije gidan aunty asiya kice nace tabani sak'on.
   Bily ta ce, "to momy, intafi da pretty??, eh kitafi da ita amma samo zani ki goyata kuma   kudawo da yanzun nan.
    Ta ce, "to.
Yau wuni guda agidan uncle G mukayi, da yamma sopy tarakamu gidan Aysha dan itama tayi aure tana nan kusa dasu, sai daredai muka dawo gida cikeda kewar yaransu masu wayo da son mutane kamar iyayensu.
      TAMMAT BI HAMDULLAH.
   
anan nakawo k'arshen littafin  NI DA AMINIYATA, kuskuren danayi ALLAH ya yafe mini, abinda na fad'a dai2 ALLAH yabani lada.

Ina k'yaunar masoyana aduk inda suke, kuma bazan manta dakuba, ALLAH yabarmu tare.


WASA KWAKWALWA.

       1⃣UMMIEE KHALEEL
daga PRECIOUS WRITERS FORUM.
      Agaskiya naji dad'in novel d'inki ba k'aramin.............shhhh bari inyi shiru ki saikin k'arasa zanyi comment.

Toni banjin tausayin ko, amma bari dai in dan tausayawa fareeda, badan halintaba, amma dan ALLAH, gashi duk ta wulak'antu, da wahala, tarasa farin ciki a rayuwar ta, ba iyaye ba miji ba AMINIYA, gata nan dai da halinta, nad'an tausaya mata dan duk bata cimma burinta ba.
     Kuma ta k'as k'antu, hak'ik'a duniya budurwar wawace kuma makaranta ce, ba sai lallai abinda wani ka yasamu kaima dole sai ka samu ba, kowa da yanda ALLAH ya tsara masa rayuwarsa.
  Rayuwa same our finger nails are not equaltausayine gare ta da bata san wannan ba.

Fareeda tafi bani haushi a cikin character wlhy kamar in kasheta .......ALLAH ya raba mu da irin kawaye mai halinta ko sama da nata.

Sopy da hubbinta nafi so, sun dace da juna kawai ba abin kad'i.

Gsky uncle G yafi burgeni his life care 2 wife, salon soyayyan shi daban yake dana sauran mazan, hakika fatan kowace 'ya mace ta samu miji mai hali irin na uncle G, nima sai da na d'an fola mashi😉.

Kada ki fada wa sopy dan ALLAH kamin ta saekeni ta sambad'a ni🏃🏻🏃🏻.

Bily 😂😂saina fad'a mata kuwa 😂.

2⃣MOMYN HUNAINA
    daga HAUSA NOVELS.
         Fareeda abin tausayi kuma abin haushi, wanda yafi burgeni dangin uncle G dasu kabeer, sai tauraruwa sopy.

3⃣RUKY B GEGAS.
     Daga PROFESSIONAL WRITER.
     Sopy tafi burgeni, fareeda kuma tafi bani tausayi, uncle G nafi so.

4⃣RUKAYYA MUH'MD daga BEST FRIEND.
    nafi tausayin sopy, nafijin haushin careers..., nafi son sopy da uncle G, sopy da uncle G da baby bilkisu sunfi birgeni.

5⃣SALAMATU B BAGAYA daga PROFESAIONAL WRITER.
      ni nafi son sopy, fareeda tafi bani tausayi, iyayen sopy kuma sunfi burgeni, saboda hakuri da sukayi da fareeda, aunty bily ALLAH yabiyaki da gidan ALJANNA da MUSLMAI.

bily....Amin salamatu ngd.

6⃣DEEXERH daga ZUMUNTA.
      babu wanda nake tausayi aunty bily, duk nafi son sopy, kuma uncle G yafi burgeni, nafi jin haushin fareeda.

7⃣TEEMA daga PROFESSIONAL WRITER.
       Assalamu alaikum, sunana teema adamawa daga pro........fareeda😰😏. Wacce na fiso sopy, team sopy, wadda yafi burgeni uncle G, aunty bily saura kicce sonshi nake.

Bily.... aii saina fad'awa sopy😜

8⃣HAUWA LELE daga PRESIOUS WRITERS FORUM.
     Nafi tausayin sopy, nafi jin haushin fareeda , nafi son sopy,  sopy tafi burgeni.
    A gsky kinyi k'ok'ari bily, sai dai gdy, ALLAH ya k'ara basira, nidai banida tacewa sai dai ALLAH ya kara basira, yakuma baki ladan wannan kokari naki.
     Taki har kullum 
Hauwa lele😘

Bily .... ngd hauwa'u, amin.


9⃣HYSH JAHUN daga SO DA K'AUNA GROUP.
     Sopy nafi so, fareeda nafijin haushi, uncle G yafi burgeni, sopy tafi bani tausayi.
      Hysh jigawa state.


🔟FASTIMA MAMMAN daga SO DA K'AUNA GROUP.
     Nima nafi son sopy, na tsani fareeda, uncle G da sopy sunfi burgeni, nafi tausayin sopy.


1⃣1⃣MURJANATU SULAIMAN daga FASHION & NOVEL GROUP.
      Nafi son sopy, wanda yafi burgeni uncle G, nafi jin haushin fareeda.

1⃣2⃣AMINA SALEH love u, daga HAUSA NOVELS.
    sopy tafi bani tausayi, fareeda tafi bani haushi, uncle G nafi so, dan yafi son sopy.


1⃣3⃣UMMUNASS daga HAUSE OF NOVEL.
    nidai sopy nafi so, kuma nafijin haushin fareeda, kuma fareeda takan bani tausayi wani lkcn.


1⃣4⃣SA'ADATU SA'AD daga HAUSE OF NOVELS.
    Nafison sopy da uncle G, gsky nafi jin haushin fareeda domin batada kirki, sannan sopy tabani tausayi lokacin da aka rabata da Abdul.


1⃣5⃣KULSUM daga HAUSE OF NOVELS.
    Nima sopy nakeso da uncle G.

1⃣6⃣NANERH daga PROFESSIONAL WRITER.
     nafi son sopy, nafi jin haushin Abdul, uncle G da uncle kabeer sunfi burgeni, fareeda tafi bani tausayi.


1⃣7⃣SAKINA GEGAS daga LEDIES FORUM.
      nafi son sopy, nafi jin haushin fareeda, uncle G yafi burgeni, fareeda tafi bani tausayi.


1⃣8⃣ UMMU MASAKEEN daga HAUSA NOVELS.
    gsky fareeda tafi bani tausayi, sannan nafi son sopy, uncle G yafi burgeni.

1⃣9⃣RUKY daga PROFESSIONAL WRITER.
      nafi son sopy, nafi jin haushin fareeda, iyayen sopy sunfi burgeni, fareeda nafi jin haushi.

ALHAMDULILLAH ina farincikin kammala wannan littafi nawa.

Ina godiya ga d'umbin masoyana, dawanda suka turomin sak'wanni da wad'andama basu sami damar turowaba, nagode da k'aunarku gareni.

Saikuma ALLAH yak'ara had'amu a sabon littafina mai suna NAWAFF DA KUKAN KURCIYA suna nan zuwa gareku nan bada dad'ewaba.


💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞 


Luv u oll😘😘😘😘😘😘😘😘😘
 ©2016us'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞



💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞

Ni Da Aminiyata! complete hausa novel

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *