Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, December 23, 2019

RAYWAR FATMA ZAHRA COMPLETE (dandalin littafan hausa)

adsense here
RAYWAR FATMA ZAHRA COMPLETE (dandalin littafan hausa)

RAYWAR FATMA ZAHRA COMPLETE (dandalin littafan hausa)

labarin.smeer: >>>RAYUWAR FATIMA ZAHRA<<< Part 1 A falo take a zaune tana kallon news, sai ya shigo yana tangadi irin ta mashaya giya, yazo ya zauna kusa da ita. Koda ta ganshi a cikin halin da ya saba shigo gida, sai hankalinta ya bar kan kallon da ta ke yi ta dube shi Cikin zubar da hawaye ta cewa, haba! Asmeer yaushe zaka daina sakani kuka ne? kullum sai ka saka ni kuka game da



wannan mummunar dabi'a taka ta shaye-shaye, kai fa ba karamin yaro ba ne. cikin magana irin ta mashaya giya ya ce mom ki daina kuka mana bana so naga kina kuka, ki cigaba da min addu'a zan...bai karisa maganar ba sai ya harar da amai mai dauke da tsamin giya wanda ya sanya hajiya tayi saurin kawar da fuskarta, sannan ta rufe hancinta. shi kuwa sai yayi kokarin ya tashi, cikintangadi ya fadi a cikin aman da yayi, sai kawai ya fara surutai marasa ma'ana har bacci ya dauke shi. hajiya da ta lura yayi bacci sai ta sakko daga kan gujeran da take zaune ta durkusa a gabansa tana kuka tana cewa ya Allah ka shiryar min da wannan yaro nawa Wanda shi kadai nake gani ina ijin dadi. jin budewar get tare da shigowar mota ne ya katsar mata da kuka da take yi. cikin saurin ta cinci6e shi ta kai shi dakin sa ta kwantar sannan ta fito ta goge wajen da yayi amai din, sai ta dakko turare ta feffesa. tayi hakanne don kare mutuncin danta, bata son kowa yasan halin da yake ciki. Bayan ta gama sai ta zauna ta cigaba da kallon news. Cikin sallama manajanta mai kula da babban kamfaninta na takalma ya shigo tare da wata budurwa mai dauke da kullin kaya. Kalle-kallen da take yi ne ya tabbatarwa hajiya budurwar bata saba shigowa irin falon nan ba. Bayan manajan ya zauna akan kujera, ita kuma budurwar ta zauna akas, sannan ta sunkuyar da kanta. Sai manajan suka gaisa da hajiya. Bayan sun gaisa cikin nutsuwa budurwar ta dago da kanta ta gaishe da hajiya. Cikin murmushi hajiya ta amsa. Sai manajan ya ce hajiya wannan ce "yar aikin da ki ka ce na nemo miki. Cikin fara'a hajiya ta ce sarki miye sunanki baiwar Allah. kanta a sunkuye cikin kunya ta ce sunana FATIMA ZAHRA amma akan kira ni da fati. cikin murmushi hajiya tace hmmm! ga suna mai dadi za a ringa kiranki da fati sai kace mai faci. sai fati tayi murmushi. sai hajiya ta ce ko dai kin fi son fati din? sai ta girgiza kai, alamar a'a. sai hajiya ta ce to ni dai fatima zan ringa kiranki ai yafi dadi ko? cikin kunya ta ce eh. shi kuwa manaja shiru yayi yana jin duk abun da suke cewa. sai hajiya ta numfasa ta ce to fatima ina fatan manaja ya miki bayanin komai? sai ta amsa da eh ya min bayanin komai. sai ta ce yauwa dan haka yau zaki fara aiki kamar yanda ya miki bayani wacce take min goge-goge jiya aka yi mata aure, shi yasa na ce manaja ya nemomin mai aiki. ina fatan ya gaya miki yanda nake biyan masu min aikace aikacen gida? sai fatima ta nisanta tare da cewa hajiya da san samu ne a ringa.... sai manaja ya hada rai ya ce a ringa miki mi? alhalin tun a mota kin amince da yanda za a ringa biyanki. cikin murmushi hajiya ta ce haba Alhaji sani "da yake sunan manajan sani" ka barta ta fadi abun da take so mana, fatima fadi abun da kike so. cikin rawar murya ta ce daman da san samu ne kar a ringa biyana kudi a ringa bani abinci ina kaiwa baaba ta, abincin ya fi min kudi. sai hajiya tayi murmushi sannan ta ce ke kuwa fatima mi yasa baki son kudi kin fi son abinci, alhalin duk ma'ikata ma suyin aiki burinsu wata ya kare a biya su albashi. ke kuma sai gashi kin fi son abinci akan kudi, saboda mi? wannan bayanin da hajiya tayi tare da tambayarta shi ya sanya idanuwa fatima suka cicciko da kwalla, sai ta sunkuyar da kanta ba tare da ta bata amsa ba. da hajiya ta lura da irin halin da fatima ta shiga sai ta tabbatar akwai babban dalilin da yasa ta bukaci abinci fiye da kudi. sai hajiya ta ce to shi ke nan fatima kar ki damu za a ringa baki abinci kina kaiwa baabar taki, sannan za a ringa biyanki albashi duk bayan wata. cikin farin ciki fatima ta dago da kanta a dai dai lokacin hawayen da ya cika idanuwanta suka zubo sai ta tashi daga ta tsugunna ta ce nagode hajiya Allah ya saka da alkairi. sai hajiya ta ce Ameen. ita hajiya ta miyar hawayen da suke fita daga idanuwan fatima ta miyar na farin ciki ne, alhalin ba haka ba ne, ta tuno da halin da suke ciki na rashi abun da zasu ci na yau balle na gobe. sai hajiya tace share hawayenki kar ki damu.Sai hajiya ta kwalla kiran diya daga cikin masu yi mata aiki. cikin sauri sai ga wacce aka aka kira, sai ta ce gani hajiya. sai hajiya ta ce Larai ki dauki fatima ki kaita dakinku. ki yi mata bayanin yanda za ta ringa goge gogen falo da gyaran dakina. cikin rawar jiki ta amsa da cewa an gama hajiya. sai hajiya ta dubi fatima ta ce ki bi larai ta kara miki bayani. sai fatima ta amsa da to hajiya, sai ta mike ta bi bayan larai. bayan su fatima sun shiga ciki sai manaja ya ja dogon numfashi ya ce kai amma mutan kauye akwai su da wuyar sha'ani. sai hajiya tayi murmushi ta ce bisa halamu yarinyar nan tana ciki halin tausayawa, amma a ina ka samo wannan budurwar mai kunya haka? sai manaja yace a nan kauyen da yake yamma da garin nan suna zaune ne a gidan yaya ta. sai Hajiya ta ce Ayyah....kiran da aka yiwa manaja ne ya katsar musu da maganar. Bayan ya gama wayar sai ya ce to hajiya zan tafi akwai bakin da nayi daga lagos suna sun suyi kodar takalma. so zan je mu gana da su. sai hajiya ta ce bakomai. sai ya tashi ya fita. FATIMA ZAHRA mace ce kyar kimanin shekara 18 Allah ya bata kyau, domin kuwa ita ba fara bace ba kuma baka ba ce ita dai wankan tarwada ce, gata da cikekken diri, tafiyarta kuwa tamkar ta hawainiya, Idan tana dari ko tayi murmushi dinfulne yake bayyana, idan ta zauna kanta a sunkuye tsabar kunyar da Allah ya bata ita kuma akidarta ce kullum kuma koda yaushe idan ta saka kayanta sai ta saka hijab wanda har kas yake ja bata yarda ta saka gyale ba, saboda kare mutuncinta, bugu da kari gata da girmama na gaba da ita. sai ita kuma bata kawowa zancen aure a rayuwarta saboda halin da suke ciki ita da baabarta. A cikin falo take sanye da burmemen hijab tana goge gogen abubuwan da suke cikin falon, sai Asmeer ya fito daga cikin dakinsa cikin shiga ta alfarma kamshin turare yana tashi. koda yazo wilgawa ta gefen fatima sai yayi arba da kyakykyawan fuskarta ai sai ya ji zuciyarsa ta buga da karfi, sai yayi saurin kawar da fuskarta daga ganin ta, sai ya doshi kofar fita amma sai ya gagara sai ya dawo ya zauna akan kujera. ita kuwa fatima ko juyowa bata yi ba, sai ta cigaba da aikinta. shi kuwa Asmeer sai ya fara tunanin ya dai na gagara fita? to ma wai wace ce wannan "yar aiki, ni dai ban santa ba kuma duk nasan " yan aikin gidan nan kuma shatu ce take irin wannan aikin kuma ita tayi aure. to wace ce wannan? tambayoyin da ya gagara samun amsoshin ke nan. sai kawai ya tashi ya doshi dakin hajiya, yana zuwa bakin dakinta sai ya kwankwasa dakin yana kiran momi. sai ta amsa, tanq dagq cikin dakin sai take cewa my dear son ka tashi ke nan? sai ya ce eh mom na tashi. sai tazo ta bude tana murmushi, tana ganinsa ta ce kai! my son ina zuwa haka? kasha kwalliya haka, kodai na kusan samun sirika ne? sai yayi murmushi yace hmmm da sauran lokaci mom. sai ta murmusa ta ce to ALLAH ya kaimu lokacin. sai ya ce ameen, yauwa mom wannan kuma fa wace ce? dan ni bansanta ba. sai hajiya tayi murmushi ta ce "yar aiki ce wacce ta miye gurbin shatu dazo manaja ya kowa min ita. sai yayi murmushi ya ce yayi kyau amma miye sunan ta? sai hajiya tace sunan ta fatima, sai hajiya ta kira fatima, cikin rawar jiki fatima ta zo ta durkusa a gefen hajiya kanta kuwa a sunkuye. sai hajiya ta dubeta ta ce fatima wannan shine dana Asmeer. cikin girmamawa ta dago da kanta ta gaishe shi, bai amsa mata gaisuwarta ba sai ya kame ya zura mata ido, domin kuwa sai yanzu ne yayi arba da dukkanin fuskarta sannan kyanta ya bayyana a gare shi, bayaga haka muryata ita ta sake rudar da shi. hajiya ce ta ta6a shi ta ce Asmeer gaisheka dai take. cikin razana ya ce au am sory lafiya kalaw. sai hajiya tayi murmushi ta cevto fatima je ki cigaba da aikinki. a tsinake fatima ta tashi ta je ta cigaba da aikinta. sai Asmeer ya ja numfashi ya ce to mom zan fita. sai hajiya ta ce to my son, amma ina zaka je haka? sai ya ce zan je walimar wani abokinmu gasi har 5pm tayi kuma tun 4:30pm za a fara. sai hajiyq ta kara murmushi sai ta ce to kai kuma yaushe za ayi taka walimar? sai ya tafi yana dariya yana cewa da saura mom. sai ta ce to a dawo lafiya sai yace Ameen. yazo kiftawa ta wajen fatima sai yakara jin zuciyarsa ta kara bugawa, haka dai ya fita yana tunanin fatima tare da mamakin yanda zuciyarsa takebugawa idan yazo wucewa ta gefenta ko idan ya hada ido da ita. .....tofa yau kam gani ga fatima zahra "yan bakin ciki sai ku mutu ehe....lolBOOKS <<>>Part 2 A cikin dakinsu suke a zaune ga fitillar acibalbal dake haska cikin dakin, a gefe kuma kunshin kayane a cikin bakar leda sai kuma shinfidu guda biyu daya taburma aka shinfida sai dayan shinfidin kuma kuntayen katifu aka jera, rufin dakin kuwa ko silin babu duk yana ya bazu ko ta ina, katangar dakin ta kasa ce ko filasta babu. bayan wadannan bakomai a cikin dakin. A zaune suke a ciki Cikin murmushi fatima ta ce da fatan kin koshi? gyada kai tayi alamar ta koshi. sai ta dakko ruwa a kofi wanda yake gefenta ta bata tasha sannan sai tayi murmushi ta ce alhmdulillah. sai ita ma ta gyara zama ta hau bawa cikinta hakkinsa. bayan ta ci ta koshi sai tasha ruwa sannan ta wanke hannunta tayi gatsa sai ta ce masha"allah. sai ta rufe sauran tuwon ta dauke shi ta ajiye a gefe ta ce wannan idan Allah ya kaimu gobe sai muyi dumame. sai ta juyo ta kalleta sannan ta ce baaba gaskiya hajiya tana da kirki, sai ta kwashe duk irin abun da suka tattauna da hajiya maman Asmeer tare da manaja har da gaisawar da sukayi da Asmeer da irin yanda hajiya ta ce zata ringa biyanta kuma zata ringa bata abinci dare da rana. Bayan ta kammala zayyana mata komai sai hawaye ya zubo daga idanuwan baabar fatima wacce ta kasance tana jin maganar da mutum yake mata amma baza ta iya magana ba, sai dai ta miyarwa mutum da amsa cikin maganar kurame. koda fatima ta ga baabarta na zubar da hawaye sai tamatso kusa da ita ta ce baaba mi ya sakaki zubar da hawaye? ke da ya kamata kiyi farin ciki. ckin zubar da hawaye ta bata amsa cikin maganar kurame ta ce "yata zubar da hawayen da kika ga ina yi na farin ciki ne ba na bakin ciki ba, sai ta cigaba ta cewa tabbas Allah ya amsa mana addu"ar mu ya kawo mana hanyar da zamu ringa cin abinci ba tare da mun fita bara ba. idanuwanta cike suke da kwalla sai da dauki hannunta ta goge mata hawayen da suke zuba daga idanuwanta sai ta ce ki daina kuka baaba haka Allah yake, yakan jarraba bayinsa ta yanda yaso, yanzu godiya ya kamata muyiwa Allah ba kuka ba. koda baaba ta ji zantukan "yarta cikin murmushi ta rungumeta sannan tana kuka. Cikin sanyi jiki fatima ta janye jikinta daga jikin sai itama a lokacin ta fara kuka tana gogewa baabarta hawayen da suke zubowa daga idanuwanta, tana cewa ki daina kuka baaba godiyawa ya kamata muyiwa Allah ba kuka ba. sai da suka dauki lokaci sannan dukkaninsu suka daina zubar da hawaye. sai baabar ta dubi fatima cikin maganar kurame ta ce bazan gaji da yi miki albarka ba ya "ya ta, ni dai a koda yaushe zanso ki zamto mai tsoron ALLAH da kare mutunciki, ki zamto mai gaskiya da rikon Amana, ki ringa girmama na gaba da ke sannan kar ki yarda a ringa hada baki da ke a cutar da wani, baya ga haka ki zamto mai taimako ga wanda bashi da shi koda kuwa ke zaki rasa abun da kike da shi inhar ya fiki bukatar taimako. idan har ki zamto mai rike wadannan abubuwan da na lissafo sannan kina amfani da su baza ki taba ta6ewa ba har a bada. koda baabar ta zo dai dai nan a jawabinta sai fatima ta ce insha"Allah baaba zan zamto mai amfani da abun da kika fada min. sai baabar ta shafa kan fatima cikin maganar kurame ta ce Allah ya miki Albarka. sai fatima tace Ameen baaba. da yake dare ya raba sosai sai fatima ta ce to baaba ya kamata ki kwanta kinga dare yayi. sai baaba tayi murmushi ciki nuni da hannunta irin ta kurame ta ce a'a sai kin kwanta sai fatima ta ce a'a baaba sai kin kwanta kafin na kwanta haka dai suka ringa yi da fatima taga haka sai ta hakura ta kwanta akan cinyar baabarta kamar yanda ta saba tun tana yarinya, saboda bata so tayi jayayya da baabarta. da baaba ta ga fatima tayi barci sai ta dauketa akan cinyarta ta kwantar da ita akan shinfidinta. sai ita ma ta kwanta akan nata shinfidin itama nan da nan barci ya dauke ta. Haka dai Fatima ta cigaba da aiki a gidan hajiya, ya zamana tana girmama hajiya tamkar mahaifiyarta bata yarda tayi late game da zuwa aikinta. sai dai idan rana yayi idan an gama abinci sai a saka mata a kwano haka zata dauka ta kaiwa baabarta duk da nisan da yake tsakanin gidan hajiya da kauyensu domin kuwa kafin kaje bayan gari ma sai kayi tafiya mai nisa, sannan ka dauki hanyar zuwa kauyen su fatima. duk da wannan nisan fatima bata taba gajiyawa ba wajen kaiwa baabarta abinci. bayan ta bata abincin rana haka zata dawo gidan hajiya ta cigaba da mata aiki har sai yamma tayi sannan sai ta karbi abincin dare ta tafi kauyensu sai kuma kashe gari ta dawo. Abun da fatima take yi wajen kaiwa baabarta abinci ba tare da ta gajiya wajen kaimata ba ko ta nuna alamar gajiya sai hakan yake burge hajiya tana jin dadi kwarai da gaske. sai ya zamana hajiya tana son fatima fiye da sauran "yan aikinta, har ya zamto tana kyautawa fatima sosai har kayan sakawa take bata, sannan haka kurin zata dauki kudi da bata tace wannan kyauta na baki. haka fatima za tayi ta godiya wani lokacin har kuka take yi idan tarasa irin godiyar da za tayiwa hajiya. ita kuwa hajiya sai ta ce kar ki damu halayenki ne sannan kuma dan Allah nake yi shi yasa nake kyautata miki fiye da sauran kyan aikina. Ita kuwa hajiya ko kadan bata bukaci ta ji tarihin fatima ba da yake babu amfanin jin tarihinta. Shi kuwa Asmeer tun ranar da yayi arba da fukar Fatima sai ya zamana kullum yana cikin tunaninta tare da mafarkinta har ya zamana ya rage shaye- shaye. kai har ya zamana yakan dawo gida akai akai, shi kansa abun yana bashi mamaki. itama hajiya tana mamkin yanda Asmeer ya canza. hakan ya sata farinciki kwarai da gaske. amma ko tambayarsa ba tayi ba dalilin canzawarsa, ita dai abun da ta kawo a ranta game da canzar danta shine shiriya ne kawai Allah ya kawo masa. kamar yanda ta saba a koda yaushe idan tayi sallah, yanzunma a zaune take akan garduma tana karatun kur,ani mai girma bayan ta idar da sallar la'asalar. tana cikin karatunne sai hajiya ta shigo cikin dakin koda hajiya taga fatima tana karatun Alkur'ani batayi mata sallama ba. ita kuwa fatima tana ganin hajiya sai ta dakatar da karatun da takeyi ta rufe kur'anin tace sannu da zuwa hajiya. cikin murmushi tace ta ce yauwa fatima, kina karatu ke nan? kanta a sunkuye cikin ladabi ta ce eh hajiya. cikin murmushi a karo na biyu hajiya ta ce yayi kyau daman inaso na ce miki idan kin idar da karatun naki ki je ki gyara dakin Asmeer yau bazan samu gyara masa dakin ba saboda zan je taziya gidan kawata. ciki biyayya ta ce to hajiya sai hajiyata juya ta ce a saka mu a addu'a. sai fatima ta ce insha'allah hajiya za a saka. sai hajiya ta fita daga dakin. fatima mamaki tayi yadda ta ji hajiya ta ce"baza ta samu damar gyara dakin Asmeer ba" cikin ranta tace daman hajiya ce take gyara dakin danta Asmeer? to saboda mi take gyara dakinsa? alhalin ga "yan aiki barkatai a gidanta, amshokin da bata samu ba ke nan sai kwai ta cika da mamaki haka dai ta yi addu'a a cikin addu'ar ta ta ta ce Allah ka biyawa hajiya bukatunta tana gama addu'ar sai ta shafa,mikewa tayi tareda nade garduman sannan ta fita ta doshi daki Asmeer don ta gyara masa dakin kamar yanda hajiya ta umarce ta. cikin dakin ta shiga jikinta a sanyaye ta fara gyara dakin, bayan ta kammala share dakin sai ta koma gyara kan gado, tana cikin gyara gadonne har ta kusa gamawa sai Asmeer ya turo kufar dakin shi gowarsa dakin ke da wuya sai ya kame tamkar wani gunki idanuwansa kuwa a kafe suke tamkar gawa. Fatima kuwa jikinta karkarwa ya fara bisa ganin Asmeer ya shigo dakin ita kuwa ko kula ba tayi da yanayin da Asmeer yake ciki ba, amma koda ta ga ya zura mata ido ko kiftawa bayayi sai kuma ta mai da hankali akan abun da Asmeer yake kallo sai ta lura Ashe ita yake kallo. cikin sauri sai ta duba jikinta don ta ga mi yake kallo a jikinta. sai ta ga Ashe gyale ne a jikinta cikin gaggawa ta tattaro gyalen ta rufe kirjinta tare da bayanta sai a lokacin ne ta tuno " Ashe ta wanke hijab dinta ta shanya shi, to shine ta sanya gyale amma da yake ta saba kullum akwai hijab a jikinta sai ta manta ta sanya gyale" ai kuwa nan da nan jikinta ya fara karkarwa sai kace a cikin hunturun sanyi. Shi kuwa Asmeer har a lokacin a tsaye yake ya kame tamkar wanda aka zare masa ruhinsa...novels / RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 3 RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 3 Posted by Bashir Sani Fesan on 27 Dec 2016 - 12:41 Ita kuwa fatima da ta ga kallon da Asmeer yake mata yayi yawa sai ta fara neman tsari daga Allah, ya kareta daga sharrin shaidan. jikinta na 6ari tayi gaggawa ta kammala shinfidin da take yi. shi kuwa Asmeer duk da fatima ta rufe jikinta da gyale bai bar kallon ta ba, domin kuwa surar jikinta a bayyane suke ba kamar idan ta saka hijab ba, sai kawar ya fara sake-sake a zuciyarsa har hadiyan yawu yake yi. Fatima tana gama masa shinfidi cikin sassarfa jikinta na rawa tazo bakin kofa da niyyar fita. a lokacin kuwa Asmeer yana bakin kofar, abun mamaki shine lokacin da fatima tazo fita kanta a sunkuye sai Asmeer ya matsa daga bakin kofar ba tare da ya cewa fatima komai ba. ita kuwa da taga Asmeer ya matsa daga bakin kofar sai tayi farat ta fita ta doshin dakinsu na masu aiki, jikinta ya rawa, ai kuwa tana shiga dakin tayi sauri ta rufe, rufewarta ke da wuya sai ta ja dogon numfashi tana fadin Alhamdulillah Allah nagode maka. Shi kuwa Asmeer da ya ga Fatima ta fita sai ya tura kofar dakin a hankali sannan ya je ya zauna a kan gadonsa, ai kuwa sai ya fada a cikin kogin tunanin fatima. A cikin zuciyarsa sai ya fara cewa Allah mai halittar abun da yake so cikin hikima da kwarewa. tabbas Allah ya zubawa fatima duk wani abun da mace take da shi wanda zai ja hankalin namiji, ga kyau, ga fasali, ga ta da dara- daran idanuwa, wow! gaskiya inhar na mallaki fatima na mallaki komai na rayuwata. tabbas duk mace mai suna fatima zahra ta amsa sunanta domin kuwa sukan kwaikwayi halayen 'yar Annabi Muhammad (S.A.W), Sannan kuma matar jarumi sayyadi Ali (A.S). cikin murmushi ya ce Insha'Allah sai kin zamto mata ta fatima. domin kuwa ke kadai ce wacce idanuwana suka fara arba har suka kaiwa zuciyata sakon sonki da kaunarki. yana gama tunaninsa sai yayi sauri ya fita ya je bakin dakin hajiya don ya sanar mata abun da yake zuciyarsa. amma sai ya kwankwasa amma sai ya ji shiru har sai da ya buga sau uku, sai ya ji shiru sai kawai ya fara kiran momi! momi!!momi!!! amma shiru dakin a kulle. sai ya ce to! ina hajiya ta je kuma? sai ya dakko wayarsa ya kira ta, koda ta dauka sai ya ce mom ina kika je ne haka nazo gida ban same ki ba ? sai ta ce nazo gidan kawata ce na yi mata taziyya. sai yace daman akwai maganar da nake so muyi ne idan kin dawo sai ta ce to sai na dawo. sai yace dan Allah ki sauri ki dawo mom yanzu nake so muyi magana. sai ta ce my son ina fatan dai lafiya kam ko? sai yace eh lafiya. sai ta ce to gani nan dawowa. sai ya kashe wayar ya je ya zauna akan kujera a Cikin falo ya daura kafarsa akan dayar kafarsa yana kadawa nan da nan ya fara tunanin Fatima yana ta bijirowa da suffan da irin kyawunta. [10:51AM, 4/30/2015] Asmeer: Ita kuwa fatima har a lokacin jikinta na rawa, shigowar Larai ne ya saka ta nutsu. Larai tana bakin kofa ta ce yamma tayi har qn kusan kiran magrib baki je kin share palo ba? Sai fatima ta mike ta dauki tsintsiya da sauran kayqn goge goge. ita kuwa sai ta juya ta doshi kitchen don cigaba da aiki. tun kafin fatima ta kariso cikin palon ta hangi Asmeer zaune akan kujera ya jingina bayansa sannan ya daura kafarsa akan dayar kafan sannan ya daga kansa sama ga kuma dan yatsa a bakinsa a lamar dai yana tunani. Ai kuwa babu shiri ta juya da baya ta koma daki. domin kuwa har yanzu tana dar dar da Asmeer. Shigowar hajiya ne ya dawo daga dogon tunanin da yake yi. cikin sauri ya mike ya ce yauwa sannu da dawowa momi. A yanayin da ta ganshi ne tayi mutukar mamaki, jikinta a sanyaye ta zauna a kan kujera ko dakinta bata shiga ba, sannan kuma bata cire hijab na taba. jakarta kawai ta ciro daga kafadarta ta a jiye a gefenta. cikin murya mai dauke da mamaki ta ce my son mike faruwa ne na ganka a cikin wannan halin? har ka bukaci na dawo da wuri. A nutse ya zauna ya kalli hajiya ya ce momi bakomai ne yasa na ce ki dawo da wuri ba sai don wata magana mai muhimmanci da nake so muyi kuma na tabbata zaki murna matuka idan kin ji abun da nake so na gaya miki. Cikin murmushi tare da cire hijab dinta ta ce to my son ina jinka gaya min abun da kake so. Cikin jan numfashi tare da cewa momi tun ranar da idona sukayi arba da fuskarta na gagara samun nutsuwa na kasance cikin tunaninta tun daga ranar da idanuwana su kayi arba da ita. ita ce macen da na fara kallo har na wanzu cikin tunanainta, dalilin hakane ya sanya kullum burina na ganta har ya zamana na daina abubuwan da nake yi sosai, kai mom ina mai tabbatar miki ta sanadiyarta na daina shaye shaye da shan giya, domin kuwa duk lokacin da nasha wani abu ko nasha giya sai naji bqbu test ko kadan saboda ina tunaninta ta dalilin haka yasa na daina shan komai burina dai na ganta na ji dadi.RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 5 Posted by Bashir Sani Fesan on 27 Dec 2016 - 12:56 : Akan mai aikin da ka kawo min wato FATIMA ZAHRA. koda manaja ya ji haka a fusace ya ce wani abun ta miki ko? kai dan adam ba a iya masa. cikin murmushi hajiya ta ce a'a babu abun da ta min, sai dai na ce fatima yarinya ce mai hankali kuma duk na fi sonta fiye da sauran 'yan aikin. Ni dai abun da nake so na ce maka shine, shin su waye iyayenta? Koda manaja ya ji tambayar da hajiya ta masa sai ya numfasa ya ce eh a gaskiya magana ban san suwaye iyayenta ba, asalima ban san daga ina suke ba, ni dai abun da zance akan fatima bara suke zuwa gidan yayata, har suka saba, to shine yayar tawa, ta tambaye su gidansu don tana kai musu ziyara, sai suka basu da gida a kwararo suke kwana, ma'ana basu da gida sai dai duk sanda suka gama barar su idan dare yayi akwai wani gidan da yake bayan kauyenmu da aka gida ba a rufa ba sai su je can su kwana. To jin hakane yayar tawa ta tausaya musu ta basu daki daya daga cikin dakunan gidanta suka zauna. To shine da ki ka ce na nemo miki "yar aiki shine na je ina gayawa yayar tawa, : Ita kuma yayar tawa shine ta je ta gayawa gaya musu, cikin murna fatima ta ce eh zata zo tana miki aikin, haka dai suka shawarta da baabar ta ta, har na dakko ta na kawo ta. to wannan kawai zan gaya miki game da fatima. koda hajiya ta ji dukkanin bayanan manaja sai ta sunkuyar da kanta ba tare da ta ce komai ba. da manaja ya ga haka sai ya ce ya naga kinyi shiru? idan wani abu fatima ta miki sai na je na same ta ita da baabarta idan fatima baza ta iya ba ta daina zuwa. kanta ta dago tare da jan numfashi ta ce a,a babu abun da tayi. shi ke nan ka tashi ka tafi office dinka na sallame ka. bai ce komai ba ya mike yana cewa to Allah ya kyauwa. Kofar fita ya dosa ya mika hannu zai bude sai ya ga fatima ta bude kofar tare da sallama, tana arba da manaja sai ta durkusa kas ta gaida shi, sai ya amsa, sannan ya ce sai yanzu kika zo? Kanta a sunkuye ta ce na tsaya na wankewa baaba ta kwayanta ne. Cikin hada fuska sai ya budi baki zai gaya mata magana, sai hajiya ta ce ya ki fatima. Kiran da hajiya tayi mata ne Ya sanya manaja ya dakata da maganar da zai yiwa fatima. sai kawai ya fita. cikin ladabi ta durkusa a gefen hajiya ta gaisheta, sai hajiya ta amsa. sai fatima ta ce ki hakuri hajiya rashin zuwana da wuri, na yiwa mamana wanki ne shi yasan ban zo da wuri ba. cikin murmushi hajiya ta ce Ayyah! ba komai fatima. A dai dai lokacinne kabeer ya fito daga dakinsa sanye da jallabiya yazo ya yauna akan kujera, zamansa ke da wuya sai ya zuraw fatima idanu yana murmushi, da hajiya da lura da irin kallon da yake yiwa fatima, sai ta cewa fatima to tashi ki je ki shirya ki zo ki fara aiki. cikin biyayya ta ce to hajiya, sai ta mike ta doshi dakinsu na masu aiki. shi kuwa kabeer binta yayi da kallo ko kiftawa ba yayi. hajiya ce ta katsar da shi daga kallon da yake mata, sai ta ce miye haka my son? cikin murmushi ya be mata ta insha'allah nake kallo. cikin sanyi jiki ta dube shi ta ce to ka janye a niyarka ta son fatima, domin kuwa sam bata dace ta zamto matarka ba. ji yayi zuciyarsa ta buga da karfi tamkar zata fito Waje.RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 6 Posted by Bashir Sani Fesan on 27 Dec 2016 - 12:58 ...ko sallama ba ta yi musu ba. Abinci take bata a cikin daki kamar yanda ta saba kullum da daddare, amma yau kwata kwata babu kuzari a jikinta. sai mamaki ya kama baabarta bisa yanda ta ga kyarta ba kamar yanda ta saba ganinta ba. sai baabar ta dakatar da fatima da ita daga bata abincin da take yi sai ta dubi fatima cikin maganar kurame ta ce "yata mike damunki yau na ganki ba kamar yanda na saba ganinki ba? cikin sanyi jiki ta dubi baabarta ta ce babu komai baaba. sai baabart ta ce to amma ya naga kin canza ba kamar yanda na saba ganinki ba? sai fatima tayi murmushi ta ce jikina ne kawai bana jin dadinsa domin kuwa yau nayi aiki a gidan hajiya. cikin maganar kurame ta sake dubanta ta ce to ai kullum ma kina aiki a gidan hajiya amma yau sai kika janza ba kamar kullum ba, ko dai akwai abun da ya faru a gidan hajiyan ne? A razane fatima ta ce eh baaba akwai abun da ya faru. sai baaba ta zare idanuwa ta ce mi ya faru "yata? cikin yanayi na tausayi ta ce baaba jiya hajiya ta tafi....bata barta ta karisa maganar ta ba, a fargice baaba ta dubeta cikin magana ta kurame ta ce ina hajiya ta tafi? cikin kyalkyala dariya fatima ta ce hajiya ta je ta unguwa jiya. sai baaba ta ja dogon numfashi ta dubeta cikin magana ta kurame ce ja'iran yarinya har kinsa gabana yafadi, na miyar ta rigamu tafiya makomar kowa ne. sai fatima ta cigaba da dariya tana cewa kai baaba kin fiye tsoro. sai baabar ta mike ta ce ai dole na tsoruta bisa jin wacce muke samun rufin a siri ta sanadiyarta ta mutu, sai ta dauki buta ta dubeta cikin maganar kurame ta ce har kinsa cikina ya kururuta dole sai na zagaya makewayi. haba! banda dariya ba abun da fatima ta ke yi. bayan baabarta ta ta fita don ta zagaya, sai fatima ta kwanta a kan shin fidarta ko abinci bata ci ba, sai ta fara tunanin abubuwan da Asmeer ya gaya mata. " Abubuwan da ta fadawa baabarta yanzu ta fadi hakanne saboda bata son gaya mata abubuwan da Asmeer ya gaya mata kuma daman abubuwa da Asmeer ya gaya mata su suka sanya ta mutuwar jikinta da rashin kuzari." jin motsin baabarta ne ya sanya ta rufe idanuwanta da sauri sai tayi kamar mai yin barci. da baabar kuwa ta shigo dakin sai ta ga fatima tayi barci, sai kuma ta dubi abincin da fatima ta kawo mata bata ci ba, cikin ranta ta ce Ayyah ko abinci baki ci ba kika kwanta? sai ta dauki murfin kwanon ta rufe abincin tana cewa a ranta idan yunwa ta dame ki ai zaki tashi ki nemi abinci, gama fadin haka ke da wuya sai itama kwanta a shin fidarta sannan ta kashe fitillar acibalbal dake haska musu dakin sai ta kwanta ai kuwa nan da nan bacci mai dauyi ya dauke ta. ita kuwa fatima ganin baabarta tayi barci sai ta mike ta zauna ta cigaba da tunanin da take yi akan Asmeer sai take cewa a ranta to mi yasa Asmeer yake sona? wanda hakan ya je fa shi cikin rashin lafiya. sannan ya ce tun sanda na je gidansu ya fada cikin wani yanayi. kai amma akwai mamaki inhar Asmeer ya ce yana sona ina matsayin "yar aikin gidansu kuma bai san ko ni wace ce ba, uhm! amma anya hajiya ta sani kuwa? sai ta bawa kanta amsa ta ce zata iya sani mana tunda shi ya ce min ta sanadiyar son da yake minne yasa ya shiga cikin halin da yake ciki kuma nasan dole hajiya ta tambaye shi mike damunsa nasan shi kuwa zai gaya mata, to amma mi yasa da ya tambaye ni ina sonsa? sai na fita da sauri ba tare da na ba shi amsa ba. Haka dai fatima ta ringa sake-sake har dare ya raba haka ta kwanta da sake saken da take yi har bacci ya dauke ta. *** *** *** A can gidan hajiya kuwa har dare yayi sosai Asmeer ya gagara bacci sai begen fatima yake yi har da rerawa fatima waka kamar haka: "Fatima zahra "yar autar mata, mai halaye da ya zarce sauran mata. *zuciya ta na baki ki rike ta ki bata kulawa don ke kika fi cancanta. *kamaninki da kyawuki da murmushiki sun rikirkita zuciyata har da hanta ta. *ki tallafa min ki agaza min ki amince min na zamto uban "ya"yanki ya "yar gata." haka dai ya ringa begen fatima da rera mata waka har aka kira sallar asuba. jin an kira sallar asuba ne ya cika da mamki yana fadin kai to yaushe daren yayi har gari ya waye? sai ya mike cikin mamaki ya je yayi alwala yayi sallah sannan ya roki Allah ya ba shi FATIMA ZAHRA. [12:09PM, 5/3/2015] Asmeer: Gari na gama wayewa kuwa hajiya ta shigo dakin Asmeer rike da kayan breakfast. koda ta shigo sai ta taras da Asmeer a kwance yana kallon silin dakin alama dai Asmeer tunani yake. har hajiya ta zo bakin gadonsa amma bai san ta zo ba. sai mamki ya cika hajiya sai ta ajiye kayan breakfast din da yake gaban gadon sannan ta taba Asmeer ta ce my son, a firgice ya ya mike koda ya ga hajiya a gaban gadonsa a tsaye sai ya sunkuyar da kansa sannan ya mata barka da safiya. sai ta amsa tare da cewa wato baza ka daina tunani ba da sa damuwa a zuciyarka bako? cikin shashshakar murya ya ce momi ke kanki kinsa bazan iya daina tunani ba da saka tunani a zuciya ta. cikin sanyi jiki hajiya ta zauna akn gadon kusa da Asmeer sai ta dube shi ta ce haba! my son shin kana son ka rasa rayuwarka ne ka sani fa inhar ka rasa rayuwarka nima zan iya rasa rayuwa ta bisa son da nake maka fiye da kaina ya dana. da sauri ya kalli hajiya a lokacin da hawaye ya cika idanunsa ya ce momi kina son nawa zaki ki da abun da nake so? momi ke kanki kinsan miye sanadiyar damuwata da kuma akan mi nake damuwa. kuma na sanar miki abun da nake so, amma sai kika nuna baki so, a hakan zaki ce kina sona alhalin baki son abun da nake so, na tabbata da Abbana yana raye zai so duk abin da nake so. cikin halin tausayawa ta dube shi ta ce my son nima ina son duk abin da kake so. ka sani fa son da nake maka ne ya sanya na hanaka son abun da bai da asali ba a san suwaye iyayenta ba da kuma daga inda suka fito, na fi son ka so mace mai asali da cantanta amma sam fatima bata cancanci ka so ta ba balantana mu hada zuriya da ita. duban hajiya ya sake ya ce na tabbata fatima tana da iyaye da kuma dangi. shin momi kinyi bincike yanda ya kamata akan fatima don sanin su waye iyayenta? cikin sanyi jiki ta ce a"a manaja kawai na tambaya. sai Asmeer ya kara da cewa to kin gani na tabbata manaja bashi da cikakkiyar masaniya akan su waye fatima? sauka yayi akan gadon ya gurkusa a gaban hajiya a yayin da hawayen da suka cika idanuwansa suka kwararo sannan ya dubi hajiya ya cigaba da cewa momina ke kadai ce gatata a rayuwa da ke nake alfahari a fadin duniyar nan ke kadai ce zan kawowa kukana ki share min, momi wallahi ina son fatima fiye da yanda baki tsammani, fatima ta zamto tamkar jinina da yake gudana a sassan jikina, fatima ita ce jagoran rayuwata idan babu fatima zan iya rasa rayuwata, ki taimaka min ki amince na auri fatima. A lokacin da yazo nan sai tausayin Asmeer ya kama hajiya sai ita ma kawai hawaye suka cika idanuwanta sai ta kama kafadun Asmeer ta tayar da shi sannan ta zaunar da shi akan gadon sai ta dubeshi tana share masa hawayen da suke zuba daga idanuwansa sai ta ce daina kuka ya dana tabbas ni uwa ce mai son duk abun da dana yake so inhar ba zai cutar da shi ba. ka kwantar da hankalinka zanyi bincike sosai kuma insha"allah sai ka auri FATIMA ZAHRA, ni dai bana so ka ringa saka damuwa a zuciyarka kuma bana so kana shaye shaye ai ka ji abun da doctor ya fada. wani irin farin ciki ne ya lullu6e Asmeer sai ya ji tamkar ya rungumeta tsabar murna amma sai ya ce nagode momina nayi mutukar farin ciki, kuma nayi miki alkawarin na daina saka damuwa a zuciyata kuma na daina shaye shaye bari ma ki gani sai ya dakko kwalbar giyan da ke karkashin gadonsa ya nufi toilet na shi da ke dakinsa ya je ya tittilar da giyan a cikin sannan ya je ya saka kwalbar a cikin dosbeen din da yake can gefe a cikin dakin. sannan ya dawo ya zauna. hajiya ganin abun da Asmeer yayi ta ce nayi mutukar murna sai ta dube shi ta ce na ji dadi kwarai da gaske dan haka yau idan fatima ta zo zan sameta muyi magana. ai kuwa yana jin haka sai yayi tsalle yana murna. sai hajiya tayi mamakinsa alhali bashi da lafiya amma yake wannan tsallen, sai ta dube shi ta ce kai da baka da lafiya kake wannan tsallen??? dariya yayi ya ce ai daman rashi lafiyar ta akan fatima ce kuma gashi kin ce zan mallake insha"allah kinga kuwa lafia ta samu. Rike baki tayi ta ce "o" yaran zamani har akan soyayyar zaku yi kokarin salwartar da rayuwarku, sai tace watakil ma ita bata sonka kamar...bata karisa maganar ba ya katsar da ita ya ce na tabbta fatima tan SO na. Abun da Asmeer dariya ya bawa hajiya sai mike tana cewa Allah yasa haka, sai ta ce to yanzu kam zaka iya cin abinci ko? sai ya ce tab da guduma kuwa bari ma ki gani sai ya mike ya zauna a kas ya dakko kayan breakfast din da hajiya ta kawo masa ya bude plate ya ga gasaassun gaji sai ya ce hmmm momi kinga da fatima ta zamto tawa da ita zata ban a bakina. sai hajiya tayi murmushi ta ce yaran zamanin baku da kunya sai ta nufi hanyar fita a dakin. sai Asmeer ya ce ya zaki fita hajiya? sai ta ce eh sakarcin nan naka ya ishe ni zan je na watsa ruwa ne. sai yayi murmushi ya ce dan Allah ni dai momi ki samu fatiman kuyi magana. sai ta hada rai ta ce basan sametan ba. ai kuwa a dai dai lokacin ya hada tea har ya kai bakinsa, cikin sauri ya feso da tea din da ya sha, sai ya ajiye kofin a gefe sannan ya matsar da naman dake gabansa cikin hada fuska ya ce to bazan ma ci ba. sai hajiya ta saka dariya ta ce kai hakuri wasa nake maka zan sme ta muyi maganar. cikin murmushi ya matso da kwanon naman tare da daukan kofin tea din ya cigaba da sha tare da cin farfesun naman kaji. ita kuwa hajiya fita tayi daga dakin ta nufi dakinta tana5] Asmeer: <<>>Part 7 ...Hajiya dakinta ta nufa tana dariya. *** *** *** cikin maganar kurame ta dube ta ta ce yanzu kan naki ya daina ciwo? murmushi tayi tana kwance ta ce eh baaba ya daina ciwo. sai ta kara dubanta ta ce to kinga har rana tayi sosai ya kamata ki tashi ki tafi gidan hajiya don yi mata aiki, navtabbata yanzu haka tana magana akan baki je kinyi aiki ba. tana daga kwance ta ce baaba ni fa yau bana so na je aiki. cikin mamaki ta ce haba! "ya ta tunda kan naki ya daina ciwo ya kamata ki je ki aiki. kinga sai kin je ne zaki samo min abun da zan ci sannan ke ma ki samu abun da zaki ci. numfashi ta ja sannan ta mioe ta zauna ta dubi baabarta ta ce haka ne baaba, amma yau din bana jin dadi sosai. sai baaba ta dube ta cikin maganar kurame ta ce ki daure dai ki je ki kin ji "ya ta. sai fatima tayi murmushi ta ce to shi ke nan baaba bari na ta shi na tafi, mikewa tayi ta dauki kwanikan abincin ta sa a leda kar yanda ta saba kullum ta saka takalminta sannan ta dauki babban hijabinta ta saka sai ta ce to baaba ni kam zan tafi sai na dawo. kallontavta yi cikin maganar kurame tavce to a dawo lafiya ki gaida hajiyan sai fatima ta ce zata ji sai ta fito a dakin da niyyar tafiya. koda ta daga daki sai ta ga yayar manaja a kwance wacce suke kiranta da hajiya rabi, sai ta durkusa a gabanta ta gaishe ta. bayan ta amsa gaisuwar fatima sai ta ce kaddai sai yanzu zaki tafi? kanta a sunkuye ta ce eh wallahi dazun kai na ne yake ciwo shi yasa ban tafi ba sai yanzu. sai hajiya rabi ta ce Ayyah! amma yanzu kan da sauii ko? sai fatima ta ce eh nasha magani da sauki. sai hajiya rabi ta ce to sai kin dawo ki cewa hajiya ina gaishe ta. cikin ladabi fatima ta ce to zata ji, sai ta mike ta nufi kofar fita. *** *** *** Hajiya a zaune take a falo tana yin waya da manajojinta na kamfanonin mijinta wanda ya rasu ya bari, a cikin wayarta ta ce take cewa eh saura sati daya a fara salari so ka tabbatar an kammala komai, domin kuwa yanzu nayi waya da babban manaja Alhaji sani mai kula da kamfanin da kalama ya gama komai, sannan nayi waya da manajan atamfu Malam ishiyaku da kuma majan da ke kula da shigowar motocin da aka iyo koda daga kwatano duk sun kammala komai saura kai da Alhaji ibrahim ne kawai baku gama shiri ba. cikin biyayya ya amsa mata da eh ranki dade nima nan da kwana biyu zan kammala koma dan haka jibi zan baro lagos din na zo ni domin kuwa tuni na sakq wadansu kudaden a banki. amsawa ta yi da ok bakomai Allah ya kaimu. sai ta kashe wayar. kashe wayarta ta ke da wuya sai fatima ta turo kofar falon a hankali ta shigo tare da sallama. hajiya tana zaune ta amsa mata. Bayan fatima ta kariso cikin falon sai ta gaida hajiya. sai hajiya ta amsa, hajiya bata ma tambayi fatima dalilin rashin zuwanta da wuri ba sai fatima ta ce ki hakuri hajiya banzo aikin da wuri ba domin kuwa kaina ne yake ciwo. cioin murmushi ta laa! bakomai ai har na saka jummai ta zo tayi aikin da kike yi, domin kuwa da na tambayi sauran "yan uwanki masu aiki na ce lafiya yau baki zo ba? sai suka ce suna tsammanin baki da lafiya jiya da zaki tafi gida ko sallama baki musu ba kuma sunga kin canza. cioin ladabi ta ce wallahi ji na yi bana jin dadi. ko tambayarta dalilin rashin jin dadin jikinta ba tayi ba sai kawai ta ce to Allah ya saukake. cikin biyayya fatima ta ce Ameen hajiya amma ki hakuri fa hajiya. sai hajiya ta kara murmusawa ta ce ah bakomai fatima. sai fatima ta ce na goee sai ta mike da nufin tafiya dakinsu na masu aiki, amma sai ta ji hajiya ta ce ki zauna mana akwai maganar da nake so muyi. cikin mamaki fatima ta dawo ta zauna kanta a sunkuye. sai hajiya ta gyara zama sannan tayi gyaran murya ta kalli fatima ta ce yauwa fatima daman maganar da nake so muyi shine na ce ki tsaya maganar kuwa ita ce fatima gaskiya kina da kyawawan halaye kuma kina burge ni kwarai da gaske ina jin dadin aikin dalilin hakane yasa na fi sonki fiye da ko wace "yar aiki a gidan nan, dan haka shi yasa nake son na je mu gaisa da mamanki. kan fatima sunkuye tayi murmushi jin an yabata an sauran "yan aiki, sai fatima ta ce hmmm...baaba ta dai ba mamana ba na ji kin ce mamana. cikin murmushi hajiya ta ce au daman baabar taki ba ita ba ce mamanki? sai fatima ta daga kanta alamar eh. sai hajiya ta ce to nikuma da mamanki nake so mu gaisa ba da baabarki ba.fatima shiru tayi ba tace komai ba, sai kawai idanuwanta suka cika da kwalla. sai hajiya ta ce ya kika yi shiru fatima? dagowar da kanta da tayi ne hawayen da suka cika idanuwanta suka zubo. sai hajiya ta gafatima na zubar da hawaye cikin mamaki ta dube ta ta ce mi ya sakaki kuka fatima? sai fatima ta ce babu komai hajiya.saihajiya ta ce haba fatima ya zaki cemin bakomai alhalin gashi kina zubar da hawaye, kodai dan na tambaye ki mamanki ne ya sakaki zubar da hawaye? kara sun kuyar da kanta tayi hawaye na zuba. sai hajiya ta dubeta cikin tausayawa ta ce ki daina zubar da hawaye mana fatima kuma gashi na tambayeki dalilin zubar da hawayenki baki gaya min ba ki sani fa duk "yan aikina ban taba tambayan mahaifansu ba sai ke kadai ke din ma saboda kyawawan halayenki ne ya sanya na tambayi iyayenki, ko dai tambayar da na miii ne ya bata miki rai har kike kuka? [11:30AM, 5/4/2015] Asmeer: cikin share hawaye tace a"a hajiya ba haka bane. sai hajiya ta ce to mi ya saka ki kuka? sai fatima tace tuno min da mahaifiyata da kika yi ne ya sakani zubar da kwalla. cikin mamaki hajiya ta ce maman taki ba ta da lafiya ne? sai fatima ta ce a"a. sai hajiya ta ce to mi ya same ta? wadansu hawayenne suka kara kwararowa daga idanuwan fatima sai ta dubi hajiya ta ce hajiya mahaifiyata bata raye ta rasu a dai dai lokacin da nazo duniya, tana zuwa dadai nan ne kuka ya ku6uce mata ta fashe da kuka. cikin halin tausayawa hajiya ta ce Allah sarki Allah ya mata rahma. cikin kuka fatima ta ce Ameen. sai hajiya ta fara rarrashinta tana cewa ki hakuri fatima. sai ta daina kuka ta fara share hawayenta. Da hajiya ta ga fatima ta daina kuka ta nutsu sai ta dubi fatima ta ce na lura da cewa idan kin tuno da mamanki ki kanyi kuka, naso na tambaye ki labarinki da kuma asalinku amma sai nayi la"akari da cewa inhar an tuno miki da mamanki ki kanyi kuka dan haka na hakura da sanin wace ce mamanki, amma abun da nake so da ke ina son ki kaini gun baabar taki mu gaisa. cikin sanyi jiki fatima ta ce hajiya tabbas kin cancanci ki ji labarina da asalina ko dan kyautatawar da kike min ni da baabata, amma kuma baabata ce ya kqmata ta baki labarina amma da yake bata iya magana ni ya kamata na baki labarin mu su waye. hajiya kuwa kallon fatima take tana mamaki. sai fatima ta cigaba da cewa labarina yafi abin tausayi akan labarin baaba, sai wadansu hawaye suka zubo daga idanuwan fatima. da hajiya da lura fatima na zubar da hawaye sanna ta gagara bata labarin sai ta ce daina zubar da hawaye "ya ta, na ga kamar baki cikin nutsuwan da zaki ban labarinki dan haka ba san kin sanar min yanzu ba. amma ki sani dana Asmeer yana mutukar sonki wannane ma babban dalilin da yasa na so na ji labarinki, dana Asmeer ya sanar da ni yana sonki amma sai na ce bazan yarda ba har sai nayi bincike a kanki hakan yasa na tambayi manaja na shine ya ce min gaskiya bashi da masaniya a kanki ke da baabarki amma sai ya gaya min iya sanayar da ya muku. ni kuwa da na fahimci cewa baku da cikekken asali sai na cewa Asmeer ya fitar da sonki a zuciyarsa. jin hakane ya sanya shi a ciki babbar damuwa da tunani, har likita yake ce min inhar ina son rayuwar dana to a ringa bashi a bun da yake so kuma a nisanci bata masa rai. to ganin tunaninki zai iya hallaka dana shine na ce ya daina damuwa ya cigaba da sonki kuma ni da kaina zan tambaye ki labarinki da kuma su waye iyayenki. to na so na je na samu baabarki ita zata fi ban cikekken tarihinki da na iyayenki. amma sai gashi na ji kince baabarki bata iya magana dan haka ke ce kadai zaki ban labarinku da na iyayenki. to shi yasa yanzu na zaunar da ke ki ban labarinki, dan haka idan kin samu nutsuwa sai ki sanar da ni labarinki. amma daga yau kin daina aiki a gidan nan sai dai ayi miki, yanzu ke zaki miye gurbin "yata Aisha. koda hajiya ta zo dai dai nan a labarina sai fatima ta cika da mamaki, sai ta ce nagode sosai hajiya Allah ya saka da alkairi, to amma na ji kin ce zan miye gurbin "yarki Aisha to amma wace ce Aisha domin kuwa ban santa ba ban kuma taba ganinta a gidan nan ba? jin tambayar da fatima da mata ne ya sanya hajiya zubar da kwalla. a kidimauce fatima ta ce ki hakuri hajiya ban san tambayar nan zata sakaki hawaye ba. cikin murmushi hajiya ta ce ba tambayarki ce ta bata min raina tunowa da mijina da Aisha su suka sakani hawaye, tunda yanzu kin zamto "ya ta dole na baki labarina don haka ki nutsu kiji labarina mai dauke da tausayi sai hajiya ta fara bata labari kamar haka: .....kai bari na nutsu na ji labarin mai ciki da tausayi kafin a zo labarin fatima zahra wanda ya ninka na hajiya sau biyar ga tausayi da al"ajabi da mamaki..HRA novels / RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 8 RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 8 Posted by Bashir Sani Fesan on 27 Dec 2016 - 13:03 ...sai hajiya ta fara bata labari kamar haka: Iyayena sun kasance talakawa, ina da yayye biyar duk maza ni ce cikon ta 6 kuma ni kadai ce mace kuma ni ce "yar auta iyayena suna nuna mana so amma kuma sun fi nuna min so fiye da yayyena kasancewa ni ce"yar auta, sai kuma a gaskiyar magana mahaifiyata ta fi nuna min so fiye da yayyena saboda ni kadaice mace bugu da kari ni ce auta. Muna da zama a jahar katsina, haka zalika iyayena haifaffun canne, yayyena basu damu da karatun boko ba sai dai dukkansu mahaifina ya tura su almajiranci har suka yi sauka suka dawo, bayan sun dawo suka fara kiwo da noma kamar yanda babanmu yake. shi kuwa da yake ya fara manyantaka sai ya zamana baya zuwa ko ina daga gida sai wajen abokanensa. ni kuwa tun ina "yar shekara goma sha biyu na daina zuwa makarantar allo haka na taso ban cigaba da karatun addini ba saboda na fara girma dan haka dole a fara tsare ni tunda ni "ya mace ce kuma har na fara girma, shi kuwa karatun boko ba a yinsa a gidanmu domin kuwa maza ba suyi ba balantana ni mace. to bayan na kai shekara 13 ne sai na hadu da Alhaji baban Asmeer muna son junan mu kwarai da gaske to shin kuwa a lokacin talakane amma shi ya gama secondry skul amma da yake iyayensa basu da kudin da zasu biya masa ya cigaba da karatu sai ya hakura da karatun boko sai kawai ya koma kasuwa wajen kasuwanci mahaifinsa suna yi tare. sannan shi ya sauke kur"ani kuma yana da ilimin addini dai dai gwargwado. domin kuwa tsantsar shakuwarmu shi yake dora min karatun Alkur"ani mai girma wani lokacin ma yakan min bayani game da karatun boko. sai dai kuma mahaifina Allah ya dora masa sun abun duniya dan haka lokacin da nakai mizanin aure har an saka mana rana da mahaifin Asmeer sai wani mai dan kudi ya fito ya nuna yana sona har yake kashewa mahaifina kudi, sai mahaifina ya fara cewa za a fasa aurena da mahaifin Asmeer tabbas jin abun da mahaifina ya fada yayi bala"in tayarmin da hankali na shiga damuwa sosai haka na je na samu mahaifin Asmeer a kasuwa na sanar masa shima kuwa hankalinsa yayi bala"in tashi. sai ya tambayeni dalilin fasa aurenmu sai na zayyana masa komai. ai kowa koda ya ji haka sai ya ringa kaiwa mahaifina kudi da kuma yi masa hidima duk don ya karkato da hankalinsa ya amince masa ya aure ni. mahaifina kuwa haka ya ringa karban kudin baban Asmeer har ya zamana jarinsu mahaifin Asmeer ya karye. shi kuwa mahaifina sai kawai ya fito fili ya gayawa mahaifin Asmeer ya hakura da ni tunda bashi da komai dan haka da mi zai rike ni. ni kuwa na ce ko kullum ruwa za a ringa sha zan auri mahaifin asmeer. amma mahaifina yaki fir sai na auri waccan. haka suma yayyena suka bi bayan babana mahaifiya ta ce kawai bata bi bayansu ba. haka dai aka daura min aure da waccan wanda bana so. shi kuwa mahaifin Asmeer ya ce ba sai iya zama a garin ba sai ya dawo nan kano da zama yana kasuwancinsa amma kuma tunda ya rasani ya dauki alwashi ba zai yi aure ba har ya mutu. na kasance cikin halin damuwa kullum sai kuka har na kasance cikin rashin lafiya amma wanna wanda ya aure ni ya ce bazai rabu da ni ba koda kuwa zan mutu. haka dai na zauna a dole amma kuma ban taba yarda ya kusance ni ba. idan yazo sai na ce bani da lafiya ko na ce masa ina al"ada haka zai hakura. bayan satin mu biyu da aure ne na je gun malami na ce ina so ya yi sanadiyar talautar da majina haka kuwa akayi ya talauce ya zamto babu abun da za a ci yau balantana na yau. da mahaifina ya ga ina shan wahala sai yasa mijina ya sake ni. sai ya bani takarda na dawo gida. ai kuwa ina dawo sai na tafi gidansu mahaifin Asmeer sai aka ce min ai ya tafi kano kuma ya koma can da zama, nayi bakin ciki sosai harma nayi niyyar binsa kano amma iyayena suka ki. haka na tashi cikin bakin ciki na rashin mallakar wanda nake so. sai ya zamna duk wanda na aura sai nayi yanda aka talautar da shi ya gara rike ni a matsayin mata, har ya zamana aka daina zuwa neman aurena ana cewa farar kafa ce da ni. ai kuwa nasha wahala sosai a gidanmu ana cewa tunda zaman gidan na fi so sai nai ta zama. Bayan nayi wata daya da gama idda ta sai baban ASMEER ya zo kallon gida nayi farin ciki sosai. haka na je gidansu da kaina muka gaisa bayan mun gama gaisawa ne na zayyane masa duk abubuwan da suka faru da ni. sai yayi murna sosai. to kafin ya koma kano sai da aka daura mana aure haka ya dauke ni yakawo ni nan garin kano. to ashe ba wata kasuwanci yake ba sana"arsa ita ce jari bola wato siyar da kayan gwangwan, amma ni hakan bai dame ni ba muka zauna da shi. ana nan sai Allah ya fara bude masa ya fara fita da cikin tirela na kayan gwangwan yana kaiwa legos na takaice miki ana nan ana nan har mahaifina ya shahara da kudi har ya zamto ana sakashi a jerin manyan "yan kasuwa kai harma ya fara odar motoci daga kwatano. A lokacin kuwa har mun haifu da shi "ya "ya biyu Asmeer da Aisher. ikon Allah kuwa tun daga kansu muka daina samun haifuwa. Muna son "ya "yanmu sosai domin kuwa karatunsu ma a kasar waje suke yi. iyayena kuwa fankacecen gida mahaifin Asmeer ya gina musu a can katsina tare da baiwa yayyena jari mai tsoka don su tafiyar da rayuwarsu. hakama iyayensa ya gina musu babban gida tare da saka musu komai na more rayuwa, duk bayan wata mukan ziyarci iyayenmu sannan mu kai musu abun da suke so. mahaifina kuwa duk sanda muka je sai yayi kuka sannn yayi tabawa mahaifin Asmeer hakuri bisa abubuwan da yayi masa a baya. amma mahaifin Asmeer sai yana cewa babu komai ai komai ya wuce har saudiya ya kai iyayena da iyayensa tare da yayyena, mijina ya kasance mai tausayin wanda bai da shi haka zai dauki ku mai tsoka ya bawq wanda bashi kai ko a hanya yaga mutum inhar ya ga alamar yana cikin halin tausayawa sai ya tsaya ya bashi kudin da mutum sai ya gagara godiya. dalilin hakane mutane da yawa suke zuwa neman taimako gunsa wani kam ma karya zai zo ya shirya. amma hakan bai hana shi kyauta ba. Na kasance cikin jin dadi da walwala duk duniya babu abu da na fiso sama da mijina da "ya "yana. ban taba sanin miye bakin ciki ba sai ranar da mijina ya bar duniya tare da kyata Aisha. a ranar sai da na kasance tamkar mahaukaciya da kyar aka samo kaina. Abun da yayi sanadiya rasuwar mahaifin Asmeer da kanwarsa Aisha kuwa shine: [12:08PM, 5/5/2015] Asmeer: Ranar da Aisher zata koma makaranta kasar waje sai Aisher ta ce yau kam dady kai zaka kai ni airport bana son driver ya kai ni sai ya ce mata a"a kyata kinga yanzu guri meeting zan je na kyan kasuwa kuma gashi kamar na kusa makara sai ta ce to ba sai ka kaini kq ajiye ba yaso sai ka wuce sai ya ce to shi ke nan tunda kin matsamin haka ya dauke suka tafi kafin su tafi airport sai da na ce zan bisu muje tare amma sai Abban Asmeer ya ce to idan mu tafi tare wa zai dawo da ni. haka dai na hakura suka tafi ai kuwa binsu nayi da kallo ina daga musu hannu har suka fice a gida. bayan sun dauki hanyar zuwa airpost sai....tana zuwa dai dai nan sai hawaye suka kwararo da idanuwanta sai fatima ta ce ki hakuri hajiya. bayan ta nutsu sai ta cigaba da ba ta labarin...to sai kawai babbar tifa ta bi ta kansu ha aka fito dasu babu rai...ai kuwa sai kuka ya kwacewa hajiya da kyar fatima ta rarrasheta. har tayi shiru sannan ta ce shi kuwa Asmeer yana can Amerca yana karatu koda ya ji labarin mutuwar mahaifinsa da kanwarsa sai ya hawo jirgi ya dawo yayi bakin cikin rasuwarsu sosai harma yake cewa ba zai koma America ba. amma bayan anyi sadakar 40 na ce ya koma tunda a wannn shekarar zai kamma karatunsa. haka ya koma ya kammala ya dawo. Babban burin mahaifin Asmeer shine ya ga sun kamma karatunsa shi da kanwarsa yayi wa Asmeer aure sannan ya dorashi a kan kasuwancinsa, ita kuwa Aisher ya ga yayi aurenta. To dalilin hakane nima na dauki alkawarin cikawa mijina burinsa akan Asmeer amma da yake yanda Asmeer yake gudanar da rayuwarsa ne yasa na hana shi gadonsa da kuma dorashi akan kasuwancin mahaifinsa saboda kar ya salwartar da su. koda hajiya ta zo nan a labarinta sai fatima ta ja dogon numfashi sannan ta ce mi dan naki Asmeer yake har kika hana shi gadonsa kuma baki dora shi akan kasuwancinsa ba? sai hajiya tayi shiru sannan ta dago da kanta ta ce fatima bazan boye miki komai ba saboda yanzu kin zamto tamkar "ya ta, dalilin hana Asmeer dokiyarsa da dora shi akan kasuwancin mahaifinsa kuwa shine Asmeer ya kasance yana shaye shaye da shan giya Amma yanzu Alhamdulillah ya shiryu ta sanadiyarki. a firgice fatima ta sanadiyyata kuma hajiya? sai hajiya ta ce eh ta sanadiyarki fatima domin kuwa son da yake miki ne ya hana shi shaye shaye. Dan haka dan Allah ki taimaka min ki amince da soyayyar dana kar ya koma shaye shaye. shiru fatima tayi sanna ta cebto hajiya yanzu dai sai na nemi shawarar baabata domin kuwa duk wani abu da zanyi sai na sanar mata idan ta yarda shi ke nan, dan ma na tabbata zata yarda ko dan abubuwan da kike mana. sai hajiya ta ce to shi ke nan hakan ma yayi kyau, shi yasa kike kara birge ni saboda son da ki ke yiwa baabar nan taki. sai fatima tayi murmushi ta ce ai dole naso ta domin kuwa na fi sonta fiye da komai na duniya ita ce tubalin rayuwa kuma ba dan ita ba da bazan kawo iyanzu ba kuma na fi sonta fiye da mahaifina da "yan uwana kuma ita baabar tawa ba ta daya daga cikin "yan uwqna kuma babu wata danganta da iyayena asali ma ita kyar aiki ce a gidanmu. cikin mamaki tare da zare idanuwa hajiya ta ce saboda mi kika fi sonta fiye da mahaifinki da "yan uwanki? sai fatima tayi murmushi ta ce amsar tambayarki tana cikin labarina, dan haka sai na shawarci baabata game da baki labarina. mamaki ne ya kara kama hajiya sai ta ce a rqnta to wannan wani irin kulawa baabar nan ta ta ta bawa fatima kuma ashe ma ba baabarta ba ce ko dangantaka basu hada ba asali ma "yar aikin gidansu ne? kai gaskiya labarinta kuwa zai kasance abun al"ajabi da mamaki aciki... Tashi da fatima blne tayi tare da cewa hajiya ana kiran kiran sallar Azahar zan je nayi sallah sannan na kaiwa baabata abinci. jikin hajiya a sanyaye ta ce to "ya ta. sai fatima ta nufi dakin masu aiki don tayi sallah. ai kuwa sai hajiya ta ce ina kuma zaki je k, ai yanzu ke kin zama "yar gida ki shiga dakina kiyi sallah. kunya ne ya kama fatima sai ta ce da kin barni nayi sallah a dakin masu aiki ai duk daya ne. sai hajiya ta hada rai ta ce to ban amince ba idan kuma nuna min za kiyi ban isa na sakaki ba to. sai fatima tq ce to shi ke nan hajiya. sai ta nufi dakin hajiya ta je ta shiga. Bayan ta idar da sallah ne sai tafi ta ce hajiya na idar. da kanta hajiya ta je ta shiga kitchen ta cika mata kulata ce gashi ki kaiwa baabar taki, sai kuma hajiya tace yau ba da kafa zaki je ba driver ne zai kai ki sannan ya dawo da ke.amma kafin ki tafi mu je daki Asmeer ku gaisa. jiknta a sanyayefatima tabibayan hajiya suka je suka shiga dakin Asmeer. [2:29PM, 5/5/2015] Asmeer: Asmeer a kwance yake akan gado yana abun da ya saba na tunanin fatima, sai kawai ya ji sallamar hajiya amma ko dagowa da kansa ba yi ba sai ya amsa sallamar. cikin murmushi hajiya ta ce ya dana ga abar begenka a kullum ta zo ku gaisa ai kuwa farat yayi ya tashi kamar wanda yayi mafarki. koda ya kyalla idanuwansa akan fatima sai ya ji wani farin ciki ya lullube shi sai ya sau wani uban murmushi sai yayi sauri ya mike ya ce fatima ga guri ki zauna sai ya nuna mata gujerar da take gefen gadonsa. cikin sanyi jiki fatima ta zauna, shi kuwa zama yayi akan kafet ya zurawa fatima idanuwa yana murmushi. hajiya tana tsaye ta yi dariya ta ce kai Asmeer ba dai madubi na kawo maka ba ka zura mata ido haka.cikin murmushi ya ce momi madubi ne mana ai ita ce madubin rayuwata. sai hajiya tayi murmushi ta ce ja"iri ko kunya babu to kai sauri ku gaisa ita yanzu gidansu zata tafi ta kaiwa baabarta abinci. cikin shauki ya kalli fatima suka gaisa. bayan sun gaisa sai yace kin amince da soyayyata ya fatima Zahra tauraruwar taurari. kan fatima a sunkuye bata ce komai ba sai kawai Asmeer ya ce ya kika yi shiru? hajiya ce ta ce kai hakuri zata gaya maka kaga yanzu hankalinta yana gun baabarta ka barta ta kaima mata abinci. sai hajiya ta kalli fatima ta ce tashi mu je gun drivern ya kaiki gidan. koda fatima ta mike sai Asmeer yayi wuf ya ce haba! hajiya ni zan kaita. sai hajiya ta ce kai da baka da lafiya Asmeer murmushi yayi ya ce ai ga maganina na. sai hajiya ta saka dariya. haka dai Asmeer ya dauki fatima a moto suka nufi kauyensu fatima. a hanyarsu ta zuwa ne Asmeer ya ringa yiwa fatima surutu tamkar wanda ya zautu, ita kuwa fatima duk abun da Asmeer ya fada daga kanta take dagawa ta ce eh a haka har suka isa Asmeer a waje ya tsaya har fatima ta shiga ta fito suka dawo. FATIMA ZAHRA sabuwar rayuwa ta bude domin kuwa ta zamto tamkar "yar hajiya wacce ta haifa, ya zamto a dakin "yar Hajiya wato dakin Aisha a nan fatima take zama duk wasu suturan Aisha su fatima take sakawa ya zamana duk abun da fatima take so koda kuwa bata tambaya ba hajiya tana bata, cikin kwanaki kalilan fatima zahra ta fito fresh ai kuwa sai kyawunta ya bayyana ta fito zinariyar mata. kai har hajiya cewa tayi baabar fatima ta dawo gidan hajiya su zauna ta cigaba da rayuwarta amma baabar bata yarda ba ta ce can yafi mata a haka hajiya ta hakura amma duk da haka hajiya tana girmam baabar fatima tamkar wanda suka fito ciki daya. duk wani abun mure rayuwa wanda baabar fatima take bukata hajiya tayi mataka. A bangaren soyayyarsu da Asmeer kuwa sun kasance tamkar masoyan juna duk da fatima bata furtawa Asmeer kalmar SO ba, amma yanda suke tare tamkar wanda su jima a cikin soyayya, kunyar da fatima take nunawa ya zamto ya ragu, hakan ya sanya Asmeer daduwar son fatima a zuciyarsa ya zamto babu wata damuwa tattare da shi. hakan yayi bala"in kwantarwa hajiya rai tayi murna sosai ganin danta ya canza sosai. Duk abubuwan nan sun faru ne a ciki kwana 6 kacal, a rana ta bakwai ne da rana fatima ta dauki abinci zata kaiwa baabarta kamar yanda ta saba, a ranar kuwa Asmeer baya gari hajiya ta aike shi katsina wajen "yan uwansu dan haka driver ne ya dauki fatima ya kaita kauyen da baaarta ta take da zama. Bayan ta shiga ne sai ta ris ki yayar manaja tana kuka sannan tana rike da takarda a hannunta. koda fatima taga hajiya rabi na kuka sai hankalinta ya tashi sai ta ce mike faruwa hajiya rabi? amma bata bata bata amsa ba tana waigawa sai taga takalman baabarta awatse a gefe da sauri ta shiga daki tana kira baaba...amma sai taji baabarta bata amsa mata ba a kidimauce ta fito daga dakin tana cewa hajiya rabi ina baabata take? ko amsa bata bata ba sai kawai ta miko mata wannan takarda dake hannunta. cikin rawar jiki fatima ta karbi ta karda da yake ta taba kartun boko sai ta fara karantawa abun da aka rubuta a takardar kamar haka: "ke fatima inhar kina son baabarki ki gaggauta zuwa babban gidan ta aka gina a nan kauyen da ke bayan gidanku, inar baki zo da wuri ba zaki zo ki tarar da gawar baabarki...... .....Wayyo mi zai faru da baabar faitim zahra...?RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 9 Posted by Bashir Sani Fesan on 27 Dec 2016 - 13:06 inhar baki zo da sauri ba zaki zo ki dauki gawar baabarki. A kidimauce ta jefar da kwanikan abincin ta ruga a guje ta nufi sabon gidan dake bayan gidansu wanda babu nisa sosai. shi kuwa drivern da ya kawota yana can gefe ya kafa kansa a kan sitiyari yana barci, dan haka bai san fatima ta fito ba har ta nufi sabon gidan da aka ce ta je ta. koda fatima ta isa bakin kofar gidan, jikinta na rawa tare da kuka ta shiga cikin gidan kanta tsaye, da yake ko kofa babu a gidan. tana shiga kuwa ta je ta taras da baabarta zaune tana zubar da hawaye, a bayanta ga wani katon mutum yana tsaye a kanta. cikin sauri fatima ta je ta rungume baabarta tana kuka tana cewa baaba babu abin da ya sameki ina??? cikin dariya wani katon namiji ya fito daga daya daga cikin dakunan dake cikin gidan, kallo daya zaka masa zaka tabbatar karkafa ne, idanuwansa jajaye fuskarsa a murtuke take tamkar wanda aka aiko masa da sakon mutuwa, fatar bakinsa kuwa ta jeme tsabar shaye shaye. gabansu fatima ya zo ya tsaya yana cewa fatima "yar kurmiya kuma talakawa, amma yanzu kuma ta koma "yar gatan hajiya....hahahahah sai ya kara turnukewa da dariya. fatima jikin baabarta ta sake sannan ta dago fuskarta ta kalli wannan katon namijin wanda yake mata magana ai kuwa tana kallon fuskarsa tayi saurin kawarwa tsabar muninsa, kanta a sunkuye jikinta na rawa ta ce haba! bayin Allah mi nayi muku kuma mi baabata tayi muku? kuka dakkota kuka kawota nan. sannan harkuka bukace ni nazo nan.? kara tuntsurewa yayi dariya sai sauran yaransa wadanda suka kewaye shi suma suka tuntsire da dariya. can sai ya murtuke fuska sai ya kalli fatima ya ce ke fatima mu "yan aika ne masu cika umarnin mai gidanmu, ta dalilinsa muka san ko ke wace ce da kuma baabarki. dan haka ba wani abu bane yasa muka dakko baabarki muka kawo ta nan sai don ki mana wani dankaramin aiki wanda zaki iyashi cikin sauki wanda inhar kika yishi zaki kubutar da baabarki daga mutuwa sannan kuma zaki samu kudi da dukkanin abun da kike so.....yana zuwa dai dai nan sai ya kwalla kiran daya daga cikin yaransa ya ce mushe miko min wannan magani. kan kace min cikin cika umarni mushe ya kawo masa wani kunshin farin gari a cikin leda. sai ogan ya mikawa fatima wannan magani sannan ya ce wannan guba ne a ciki. aikin da nake so kiyi shine gobe da yamma Asmeer zai dawo daga katsina, sannan kuma nasan tare kuke cin abinci da shi da hajiya dan haka ki san yanda kika saka musu wannan gubar a cikin abincin da zaku ci gobe da daddare inhar sunci baza su wuce awa daya ba a duniya za su mutu. fatima tana jin haka sai tayi sauri ta ja da baya tare dafe kirjinta, wani dogon numfashi ta ja muryata ta rawa ta ce a"aaa gaskiiiyyyaaa baaa zaaan.....kafin ta karisa maganar ta wannan katon mutumin ya daka mata tsawa ya ce zaki iya inhar kuwa baki aikata hakan ba to ina mai tabbatar miki jibi da safe zaki zo ki taras da gawar baabarki a nan. yana gama fadin haka ya wullawa fatima kunshi maganin a gabanta sannan ya ce inhar kina son baabarki fiye da komai a duniya kamar yanda kika fadawa hajiya to ki aikata abun da na umarce ki idan kuma baki sonta to kina fita a gidan nan ki jefar da wannan kullin gubar...yana gama fadan haka ya umarci wannan katon yaron nasa da ke bayan baabar fatima da ya dauketa ya sakata a dakin da ke bayansa. cikin cika umarni ya tayar da ita ya nufi da ita dakin dake bayansa. fatima fashewa tayi da kuka tana fatin karku kashe min baabata ku taimake ni. ita kuwa baabarta ta girgizawa fatima kai take yi tana kuka alamar kar ta aikata abun da suka umarce ta. har aka shiga da ita wannan dakin. shi kuma ogan tare da sauran yaransa dariya suke yi har suka shige dakunan gidan suka bar fatima zaune tana kuka. Fatima ganin an shiga da baabarta wannan dakin sai da ta dauki tsawo minti biyar tana zaune tana kuka tana fadin karku kashe min mamana kar ku cutar da ita...a dole ta tashi ta doshin hanyar fita tana tafiya tana kuka sannan tana tangadi tamkar wacce ta sha giya. haka ta fito daga gidan tana kuka ta doshi wajen driver kai tsaye, koda ta kusan isa gunsa sai tayi sauri da goge hawayen dake zuba daga idanuwanta sannan ta dai daita tafiyarta ta zamto tamkar babu abun da ya faru da ita, sai dai kuma jikinta a sanyaye sannan idanuwanta sunyi ja alamar tayi kuka sosai. wajen driver ta nufa ko gidansu bata waiga ba. koda ta iso wajen drivern sai ta taras da shi yana barci. koda ta ga haka sai tayi masa magana cikin shashshakiyar murya a firgice ya tashi yana cewa har kin kin fito ranki dade. koda ta ji wannan tambyar daga wajen driver sai ta fahimci cewa ashe bai san lokacin da ta fito ta je gidan da aka tsare baabarta ba. dan haka sai ta ji dadin hakan cikin rawar jiki ta ce eh na fito sai ta bude kofar motar ta shiga. shi kuwa ko kula bai yi da yanayin da fatima take ciki ba yayiwa mota key ya tayar da ita suka nufi cikin gari. kai tsaye gidan hajiya driver ya nufi don miyarwa da fatima. [10:48AM, 5/7/2015] Asmeer: Bayan sun iso gidan hajiya. jikin fatima a sanyaye ta fita a motar da shiga cikin gida. tana shiga ciki sai ta taras da larai tana goge falo koda larai ta ga fatima ta shigo sai ta ce sannunki da dawo ranki dade. da kyar fatima ta amsa mata sannan sai ta nufi dakinta wanda yake saman beni beni koda ta zo bakin matakalar da zata kaita dakinta sai larai ta ce ranki dade hajiya ta ce na gaya miki ta tafi wajen taron da suke yi duk bayan wata daya don biyan ma"ikatanta na kamfanoninta da na gida albashinsu. shine ta ce idan kin dawo na gaya miki, sannan abinciki yana cikin dakinki hajiya ta kai miki. cikin sanyin jiki ta amsa da to. sai kawai ta hau matakalar ta doshi dakinta. tana shiga daki da zube akan gado ta kifa kanta sannan ta fashe da kuka tamkar baza ta daina ba. can zuwa wasu mintuna ta daina kukan sai ta dago ta kanta ta fara tunanin wadan nan mutanen tana cewa to shin wani azzalumi ne ya saka wadannan mungayen mutanen don su sakani mummunan aikin da bazan iya ba? to miye ribarsu na kashe Asmeer da hajiya? idan sun kashe su wani abu zasu samu? kai duk yanda za ayi wani na karkashin tane yake so ya kashe su don ya mallaki dukiyar hajiya da na danta. haka dai ta ringa tunani har aka kira sallar la"asar akayi salla sannan yamma ta shiga. amma fatima tana kwance tana zubar da hawaye tare da tunani. kwankwasarwar da akayi a kofarta ne ya katsar mata da tunanin da take yi. sai kawai ta ji muryar hajiya tana cewa "yata "yata ko dai barci kike yi ne? cikin rawar jiki ta mike ta zauna sai ta fara goge hawayen da suka cika fuskarta sannan ta tashi ta shiga toilet din dake dakinta ta wanke idanuwanta. amma duk da haka fuskarta ta kumbura idanuwanta sunyi ja. sai ta je ta bude kofar tare da cewa sannu da dawowa hajiya. cikin murmushi hajiya ta ce ya naga fuskarki ta kumbura kuma idanuwanki sunyi ja kodai duk baccin ne? cikin kame kame ta ce eh bacci da nayi ne. sai hajiya ta ce to zo muje falo ina dauke da wasu abubuwan da na siya miki. cikin sanyi jiki fatima ta ce to hajiya. zamansu ke da wuya sai hajiya ta dubi fatima ta ce ina fatan larai ta gaya miki inda na je? cikin murmushi fatima ta ce eh hajya ta gaya min. sai hajiya ta ce to albishirinki! cikin mamaki fatima ta ce goro. sai hajiya ta ce fari ko ja? cikin karfin hali fatima tayi murmushi ta ce fari. sai hajiya ta ce to rufe idanuwanki. cikin mamaki fatima ta rufe. sai hajiya ta fiddo da key din mota tare da wasu takardu a cikin ambulov. sai ta cewa fatima bude idanuwan naki. cikin kunya fatima ta bude sai ta ga hajiya ta miko mata key. sai hajiya ta ce hungo karbi. cikin mamaki fatima ta karba sai hajiya ta ce bayan mun tashi a taron da muka yi ne nabi ta wajen siyar da motocin Mahaifin Asmeer na dakko miki wannan key din sabuwar mota Anaconda na kawo miki taki ce na mallaka miki ita ga car motar a pake a wajen parking din motocin gidannan, sannan munyi waya da Asmeer ya ce da kansa zai koya miki motar. wannan kuma ambulov din takardun account din ki ne wanda na bude miki a first bank tare da cheque a ciki, naira million biyar ne a cikin account din. duk naki ne. sai hajiya ta kara dakkowa wata katuwar ipad ta mikawa fatima ta ce wannan kuma Asmeer ne ya ce na siya miki yana son kuna waya dan haka itama taki ce, sannan akwai kayayyakin da Asmeer ya ce zai siyo miki a katsina gobe zai tafo miki da su. sai hajiya ta janyo wata akwati a gefenta ta mikawa fatima wannan kuma ba naki ba ne na baabarki ce gobe in Allah ya kaimu ni da kaina zamu je mu gaisa sannan na ba. hajiya tana gama mikawa fatima dukkanin abubuwan da ta siya mata ita da baabarta sai ta ga fatima ta fashe da kuka tamkar baza ta daina ba. sai hajiya ta ce miye abun kuka fatima ai kinfi haka a guna shi yasa na siya miki dukkanin wadannan abubuwan, sai hajiya ta matso kusa da fatima ta rungumeta a kirjinta tana rarrashinta tamkar karamar yariya..... ....tab yau ake yinta fa, fatima ta fada a cikin tsaka mai wuya. ya ke nan?MA ZAHRA novels / RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 10 RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 10 Posted by Bashir Sani Fesan on 27 Dec 2016 - 13:08 hajiya tana rarrashinta tamkar wata karamar yarinya. Fatima kuwa kuka ta cigaba da yi babu kakkautawa tamkar baza ta daina ba. Da hajiya ta ga kukan yayi yawa sai ta ce haba! fatima wannan wani irin kuka ne? kiyi shiru mana. "ita hajiya ta dauka kukan da fatima take yi na farin ciki ne bisa abubuwan da tayi mata, amma sam ba haka ba ne. tana kuka ne akan abun da mungayen mutanen nan suka saka ta ne tare da halin da baabarta take ciki. Hajiya da ta ga kukan fatima yayi yawa sai ta kwalla kiran larai ai kuwa tamkar daman wacce tasan za a kirata sai ga ta tashigo falon cikin biyayya ta durkusa ta ce gani hajiya. sai hajiya ta ce maza debi wadannan kayayyakin ki kaisu daki fatima. cikin biyayya ta ce to hajiya. ita kuma hajiya sai ta tasar da fatima ta kama hannunta suka je suka hau matakala suka doshi dakin fatima. Bayan hajiya ta zaunar da fatima akan gado sai ta ce fatima ki daina kuka mana tun muna falo kike kuka gashi mun shigo dakinki baki daina ba, wannan kukan da kike yi har ya wuce na farin ciki, ko dai akwai abun da yake damunki ne? koda fatima ta ji abun da hajiya ta ce mata sai ta sassauta kuka. sai hajiya ta cigaba da cewa inhar akwai abun da ke damunki nima uwa nake gare ki, ki sanar min shi don mu magance shi. sai kawai fatima ta daina kuka ta dago da kanta cikin shishshitun kuka ta ce babu komai hajiya.kulawar da kike bani ni da baarta ba mu san irin godiyar da za mu miki ba, domin kuwa kin mana komai sai dai mu ce Allah ya saka miki da alkairi, Allah ya kare ki ke da danki da dukiyarku gabaki daya. hajiya murmushi ta sau sai ta ce Ameen "ya ta nagode da wannan addu"ar taki, dan haka gobe da safe sai ki zo da wuri don ki kaini gun baabarki mu gaisa. koda fatima ta ji haka sai tayi shiru ta sunkuyar da kanta. sai hajiya ta ce ya kika yi shiru? sai fatima ta nisanta kadan sai ta dago da kanta ta ce ai baabata ba ta nan ta tafi garinmu kallon gida. cikin mamaki hajiya ta ce daman kuna da "yan uwa a garinku? sai fatima cikin sanyi jiki ta ce eh. sai hajiya ta ce ina ne garin naku? cikin sanyin jiki ta ce garin mu shine AZARE can jahar BAUCHI. sai hajiya ta ce Ayyah to yanzu yaushe za ta dawo? sai fatima ta ce nan da kwana uku. sai hajiya ta ce to amma mi yasa da zata tafi baki gaya min ba? ai da na saka driver ya kaita. muryar fatima na rawa ta ce eh nima dazu da na je gida ne na taras ta tafi ban san ta tafi ba. cikin mamki hajiya ta ce au baki san ma ta tafi ba. to mi yasa bata gaya miki ba? alhali bata da kowa a nan sai ke kuma ke kika fi cancanta ta gaya miki. Fatima ji tayi kanta ya fara ciwo sai kawai ta kama kanta. sai hajiya ta ce lafiya kuwa kika kama kanki? sai ta ce wallahi kan nawa ciwo ya ke yi. sai hajiya ta ce subhanallahi! to bari na kira larai ta kawo miki magani a dakina. sai ta kwalla kiran larai. sai larai ta amsa. nan da nan sai larai ta shigo dakin ta durkusa a gaban hajiya ta ce gani. sai hajiya ta ce maza je ki cikin dakina a cikin durowa da ke gefen gadona ki dakko min panadol extra, maza ki Sauri. cikin rawar jiki larai ta fita ta doshi dakin hajiya. sai hajiya ta fara cewa sannu fatima. hannunta rike da kanta ta ce yauwa sannu. hajiya tana cikin cewa fatima sannu sai ta kyalla idanuwanta akan abincin da ta kawo fatima sai ta lura yanda ta kawo abincin haka suke ba a taba su ba. sai ta ce fatima daman baki ci abinci ba ne? jikinta a sanyaye tace eh ban ci ba saboda bacci ne ya dauke ni dazun. sai hajiya ta mike da dakko abincin sannan ta kawo gaban fatima da kanta ta bude abincin ta fara zubawa a plate. a dai dai lokacin ne larai ta turo kofar dakin ta shigo ta durkusa a gaban hajiya ta mika mata maganin, sai hajiya ta karba bayan ta karba ne sai larai ta ce kawo na zuba abincin mana hajiya. sai hajiya ta ce a"a ki barshi zanzuba da kai na ke dai jeki ki cigaba da aikinki. haka larai ta mike ta fita cike da mamakin yanda hajiya take dawainiya da fatima da baabarta har take ayyanawa a ranta cewa anya ba asiri fatima da baabarta su ka yiwa hajiya da danta ba? haka dai ta ringa sake sake har ta koma kitchen ta cigaba da aikinta. Bayan hajiya ta gama zuba abincin a plate sai ta mike ta zauna a kan gado kusa da fatima sai ta debo a cokali da mikawa fatima a bincin a bakinta tana cewa maza ki ci ina tsamman ma yunwanne ta saka miki ciwon kai. cikin kunya fatima ta ce a"a hajiya kawo zan ci da kaina. hajiya harara ta bugawa fatima sannan ta ce a"a hungo ki ci. cikin kunya fatima ta ci a bincin da hajiya ta miko mata. haka hajiya ta cigaba da bata tamkar karamar yarinya ita kuwa fatima hawaye take zubarwa ganin yanda hajiya take bata kulawa tamkar "yar da ta tsugunna ta haifa. chokali uku hajiya ta bata sai fatima ta ce ta koshi. sai hajiya ta ce a"a ki dada dai.sai fatima ta ce ta koshi haka dai hajiya ta barta sannan da bare magani ta zuba ruwa a kofin sannan ta ce to gashi kisha maganin. haka fatima ta karba tasha magani. sai hajiya ta ce to ki tashi ki wanka sannan kiyi sallah kinga magrib tayi. sai fatima ta ce to hajiya. sai a lokacinne fatima ta tuno ba tayi sallar la"asar ba. cikin sauri ta mike ta shiga toilet don yi alwala. ita kuwa hajiya tashi tayi ta debe kwanikan abincin ta fita a dakin fatiman. [11:10AM, 5/9/2015] Asmeer: A cikin wannan dare fatima kwana tayi ba tayi barci ba l, a kwance take tana kuka sannan tana tunanin mummunar aikin da aka sakata, can cikin zuciyarta ta fara cewa a gaskiya inar na kashe uwar gijiyata "wato hajiya" to ban nuna halacciba, tabbas hajiya ita ce ta zame mana jigon rayuwa a yanzu ni da baabata , kuma fa ta sanadiyar danta muka samu kanmu a wannan rayuwa mai dadi domin kuwa ba dan danta ya ce yana sona ba da bazan samu kaina a wannan rayuwa ba. dan ha inhar na kasheta ita da danta babu makawa zamu tsinci kaina cikin kunci da bakin ciki, kuma baza taba jin dadin rayuwa ba har na mutu. to sannan inhar anyi bincike aka gano ni na kashe su shi ke nan ni kam tawa tazo karshe. To amma fa baabata ita ce tushen rayuwata domin kuwa ba dan ita ba da ban kawo wannan lokacin ba. tun ina yarinya ita ce ci na sha na suturata da dai sauran kulawar da iyaye ke bawa "yarsu. bugu da kari baabata tafi min mahaifina da sauran dangina gabaki daya dan haka mi zai sa na bari a kashe min baabata? kai! wannan wani irin masifa ce sai kawai ta fashe da kuka.. ta jima tana kuka sannan ta tashi ta je tayi alwala tayi sallah raka"a biyu sannan ta nemi mafita daga Allah sannan ya kare mata baabarta daga hannun azzaluman nan. haka ta ringa addu"a har aka kira assalatu. Bayan tayi sallar asuba ta kara rokon Allah, har gari ya waye. Da sassafe kuwa sai ga hajiya a dakin fatima rike da kayan breakfast. bayan sun gaisa sai hajiya ta mikowa fatima wayarta ta ce gashi Asmeer yana son waya da ke. cikin sanyi jiki ta karbi wayan. ai kuwa karbar wayar ke da wuya sai Asmeer ya kira. jikin fatima na rawa ta dauki wayan. muryarta a shake suka gaisa da Asmeer. koda Asmeer ya ji muryarta a shake sai yace my life mike damuki na ji muryarki haka? sai ta ce a"a yanzu na tashi a barci shi yasa. sai ya ce anya kuwa idan akwai abun da yake damunki ki gaya min bana son wani abu ya ringa damunki. cikin sassanyar murya ta ce babu abun da yake damuna yayana. sai ya ce amma mi yasa baki bude wayar da momi ta baki ba, akwai sim a ciki fa. sai ta ce mantawa nayi amma insha.allah yanzu zan bude ta. sai ya ce yauwa please ki bude wayan ki fara using da ita. sai fatima ta ce to. sai ya kara cewa yauwa my life mi zaki dafa min yau domin kuwa bana son girkin kuwa sai naki, na fi son girkinki ya fara shiga cikina idan na dawo. sai tayi murmushi ta ce to mi kake so a dafa maka? sai ya ce hmmm.abu mai dadi. sai fatima ta ce to na dafa maka jelof rice? sai ya ce wow my best food. ya akai ki kasa nafison jelof rice sai ta ce hmmm..hajiya ce ta gaya min. cikin sauri hajiya dake kusanta ta ce kar ki min karya ba ni na gaya miki ba ke dai daman kin sani. sai fatima tayi murmushi ta ce masa wani lokaci zaka dawo? sai ya ce eh around 5pm zan shigo kano saboda 11qm zan ta so. sai fatima ta ce to Allah kawo ka lafiya yayana. sai ya ce Ameen. sai hajiya ta ce miko min wayata kar ki cinye min kudina, ku idan kun fara waya sai ka ce baza ku daina ba. sai fatima ta mika mata wayar ta ce ga wayarki nima ina da tawa ai. sai hajiya ta ce eh dai a ban tawa, bari ma kika ga na tashi na je na watsa ruwa amma kan naki ya daina ciwo ko? sai fatima ta ce eh ya daina. sai hajiya ta ce Allah ya kara miki lafiya. sai hajiya ta fita. ita kuwa fatima ko waigar kayan breakfast din da hajiya ta kawo mata ba tayi ba sai ta dan shingida ai kuwa sai barci ya dauke, bata tashi ba sai da aka kira sallar Azahar, ai kuwa tana tashi sai ta ji wani irin yunwa. nan da nan ta fara cin wannan kayan breakfast din. duk da ya huce haka ta ci saboda yunwa. Can wajen karfe 5:30pm sai ga Asmeer ya shigo da motarsa cikin gidan. yana parking mota sai ya kira mai gadi yazo ya shiga da kayan da ya zo da su cikin gida. haka kuwa akayi driver ya shiga da dukkanin kayayyakin ciki. Asmeer yana shiga cikin gidan sai ya tarar da hajiya da fatima zaune a falo. yanda ya ga fatima ne ya ce wow very councious build gaskiya kinyi kyaw my sister. ita kuwa mamki tayi saboda ba wani kwalli tayi ba iyaka wanka tayi ta saka kaya amma ya ce tayi kyaw. "ita abun da fatima bqta sani ba ko ba tayi wanka ba kyau take da shi balanta tayi wanka, ai idan tayi kwalliya kuma shi kansa Asmeer ba zai i control din kansa ba tsantsar kyan fatima zahra". bayan Asmeer ya zauna hajiya da fatima sukamasa sannu da dawo sannan ya ce su kq sunce a gaida ke. sai hajiya ta ce amsawa. Bayan Asmeer ya danyi surutansa sai hajiya ta ce to ka tashi ka je kayi wanka ka fito ka ci abinci haka ya tashi ya shiga dakinsa. Bayan sallar isha"i ne hajiya da fatima suka zauna a wajen da suke cin abinci suna jiran Asmeer ya fito su ci abinci. ita kuwa fatima zuciyarta sai bugawa take bisa ayyana cewa yanzu ne fa dadai lokacin da za ta sakawa hajiya da Asmeer wannan gubar kamar yanda aka umarce ta. tana cikin wannan tunanin ne Asmeer ya fito daga dakinsa bayan ya zauna sai hajiya ta ce mi ka tsaya yine hak tun dazu muke jiranka. bude bakinsa yayi zai yi magana sai aka kira shi a waya sai ya dauki wayan. bayan yi wayar sai ya shi ya ce momi am sorry wani friend nawa ne muka hadu a katsina ya ban wani sako ya ce na kai gidansu kuma gobe da sassafe ake son ayi amfani da sakon so bari nayi sauri na kai sakon na dawo. yana gama fadan haka sai ya kalli fatima ya ce sister na ki hakuri bari na je na dawo. [11:22AM, 5/9/2015] Asmeer: kanta kawai ta daga ba ta ce komai ba. cikin sauri ya fita a gidan. Bayan wasu lokuta sai kawai hajiya ta ji fatima tana kuka. cikin mamaki hajiya ta kalli fatima ta ce "ya ta lafiya kike kuka? cikin kuka fatima ta tashi daga kan kujerar da take zaune ta ce hajiya yau ce ranar da tafi cancanta ki ji labarina wanda yake cike da tausayi da al"ajabi, baya ga haka idan na baki labarina akwai tambayoyin da zan miki wanda ina son ki ban amsansu. cikin mamaki hajiya ta mike ita ma daga inda take zaune sai kawai tabi fatima da kallo sannan ta ce ina jinki ya "ya ta kuma na miki alkawari zan gaya miki tambayarki dai dai da tambayarki inhar nasan amsoshinsu. sai fatima ta cigaba da kuka sai kuma ta budi baki ta fara bata labarinta kamar haka: ....uhmmmm an zo gurin kun nutsu kuji labarin mai cike da tausayi da al"ajabi.IMA ZAHRA novels / RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 11 RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 11 Posted by Bashir Sani Fesan on 27 Dec 2016 - 13:16 sai fatima ta fara bata labari kamar haka: Ni na taso na ganni a hannun baabata a wannan gari na kano tana bani dukkanin kulawa tamkar "yar da ta haifa, har islamiyya ta sakani, a lokacin tana magana tamkar yanda kowa yake magana kuma a gidan kakarta ta wajen uwa muke zaune, baabata ita take sana"o"i dabam dabam kamar su siyar da kayan miya, sirfe, har sissika take yi don ta samu kudin ta zata ciyar da ni da kakarta sannan duk wani dawainiyar islamiyyata ta biya. haka na taso cikin kulawa, kakar baabartawa tana sona sosai domin kuwa a kan shinfidartama nake kwana sannan har abinci muke ci. Akwai watarana bayan na kai shekara 10 a duniya bayan na dawo daga islamiya kuma a ranar ne aka mana hutu sai na zo na samu baabata a daki tana zaune tana cin abinci, kakar baabar tawa ku tana bacci. ko kayan islamiyyata ban cire ba na zo da gudu na rungume baabata ina murna sai take ce min "yata murnar mi kike haka kodai duk murnar hutunne? sai na ce bayan murnar hutun ma kin ga sai na mika mata report card dina na ce mata kinga wannan jarabawarma ni nayi na daya. cikin murna ta daina cin abincinnata ta kara rungumeni tana cewa "yata Allah ya miki albarka bisa kokarin da kike da shi na karatu tun da na saki a makaranta ke ki ke yin na daya har wajen Quiz ma ke kike ciyowa sannan kuma a musabakar Al- kurn"ani ma ke kike zamtowa tauraruwa kai babu abun da zan cewa Allah sai godiya, sai kawai hawaye suka fara zubowa daga idanuwanta, da na ga tana zubar da hawaye sai na shiga goge mata ina cewa ki daina kuka baaba. haka ta daina kuka bayan ta daina zubar da hawaye sai na koma gefe na zauna kusa da ita nayi tagumi. koda ta ga halin da nake ciki sai ta ce "yata mi yake damunki haka na ga kinyi tagumi alhalin na daina zubar da hawaye. sai na ce mata ba haka ba ne. sai ta ce to mike damunki? sai na ce mata yau ne malamin mu bayan munyi assembly yake ce mana kunga wannan hutun da aka muku ba wai an muku ba ne don ku je ku kwanta ko kuna wasa an muku ne don ku je kuna taimakawa iyayenku sannan kuna karatu a gida baya ga haka kuna ziyartar "yan uwanku da abokanenku da marasa lafiya da sauran "yan uwanku to duk wanda baya ziyara idan yazo tsallake siradi wutar jahannama zata janyo shi ya fada ciki. to da na ji haka ne shine na zo gunki ki kai ni wajen "yan uwanki da na baabana na ziyarce su, koda baabata ta ji bayanin da na mata sai na ga ta daina cin abincin jikinta a sanyaye ta ce min hakane abun da malaminku ya gaya miku, amma ki hakuri zan kai ki . raina a 6ace na ce kullum ha kike gaya min idan na ce ki kai ni wajen "yan uwanku sai ki ce sai anyi hutu to gashi anyi hutun ai. cikin rarrashi ta ce min fatima na kuma "yata ta kaina zan kai ki wajen "yan uwana da na babanki. ke dai ki je ki cire kayan makarantarki ki je ki dauki abincinki ki ci sannan kiyi wanka. raina a bace na ce mata bazan ci komai ba yau inhar baki kai ni wajen "yan uwanki ba da na babana. haka dai ta ringa rarrashina amma naki. sai nake ce mata baaba kinga bana son wutar Allah ta ci ni ni da ke saboda malamanmu suna ce mana wutar Allah tana da zafi sosai tafi ta duniya sosai nesa ba kusa ba. ko dai kina so mu shiga wutar ne? sai baabata ta ce a"a bana so. sai na ce mata to ki kai ni wajen "yan uwanki da na babana. sai naga baabata tayi shiru sannan sai naga ta dago da kanta hawaye na zuba sai ta ce min "yata tabbas yau ne zan sanar miki sirrin da na buye miki wanda nayi niyar bazan taba sanar da ke ba, amma sai gashi yau zan sanar miki, sanar da ke shine mafi cancanta da kaucewa daga fushinki. dan haka ki saurara da kyau ki ji labarin da zan gaya miki wanda shine labarinki da na iyayenki domin kuwa ba ni ba ce mahaifiyarki. jin abun da baabata ta fada sai na zaro da idanuwa sannan na nutsu na ce mata to wace ce mahaifiyar tawa idan ba ke ba? cikin yanayi na tausayawa ta dube ni ta ce eh bani bane mahaifiyarki amma dai yau kuma yanzunnan zaki ji ko wace ce mahaifiyarki. sai nayi shiru na zura mata idanu ban ce mata komai ba. sai ta dube ni ta fara cewa [11:42AM, 5/10/2015] Asmeer: Iyayenki da "yan uwanki haifaffun Azare ne da ke can jahar Bauchi, nima haka a can nake ni da "yan uwana. Mahaifinki mai suna Kamal da mahaifiyarki mai suna Fatima masoyana ne sosai suna son junansu kwarai da gaske, domin kuwa samari da yawa suna cincirindo akan mahaifiyarki saboda kyawun da cikar suffar da Allah ya zubawa mahaifiyarki, shi yasa duk namijin da ya ganta baya iya rabuwa da ita sai yamata magana amma bata sauraron kowa duk wanda ya matsa mata sai ta ce an bayar da ita ga mahaifinki haka dai ta rike amanar soyayyar mahaifinki kwarai da gaske. haka suka cigaba da soyayyarsu mai ban sha"awa domin kuwa "yan mata da samari har kwaikwayar soyayyarku suke ke harma aka sakawa iyayenku hanta da jini babu mai iya rabaku sai Allah. bayan sunyi nisa sosai a soyayyarsu sannan a lokacin mahaifinki ya kammala karatunsa har ya samu aiki a asibin F.M.C da ke can Azare sai ya bukaci aurenki har aka bashi ke aka yanke muku ranar aure. to tunda gada wannan ranar mahaifiyarki ta dai fita balantana wani ya ganta har ya mata magana. mahaifnki ne kawai idan yazo take fita shi din ma ba a waje suke fira ba akwai wani daki a zauren su mahaifiyarki a nan suke shiga suyi firarsu. Ana sauran sati daya ne bikin su iyayenki sai mahaifinki ya kira mahaifiyarki dakinsa dake bayan gidansu. babu shakkar komai mahaifiyarki ta je gunsa. bayan ta je ta sai ta ga ya canza ba kamar yanda yake kullum ba. sai yake cewa ce mata gaskiya yau a matse yake sosai. sai mahaifiyarki ta ce ba ta gane mi yake nufi ba. tun yana sake sake da kame kame har ya fito fili ya bayyana mata cewa gaskiya shi yana son ya kwanta da mahaifiyarki yanzun nan. koda mahaifiyarki ta ji haka sai hankalinta ya tashi take ce masa haba! masoyina uban "ya "yana kai hakuri mana saura sati daya ne kacal ayi auren na mu fa, idan munyi aure sai kayi abun da ka ke so da ni. Mahaifinku kuwa hankalinsa ya tashi sosai dan haka sai idanuwansa suka rufe ya ce inhar baki amince na kwanta da ke ba kar ki kara nunawa kin sanni. koda ta ji haka sai ta fashe da kuka sai ta juya zata tafi, koda ta je bakin kofar fita. sai mahaifinki ya tashi ya ce inhar baki bani hadin kai ba kika fita daga dakin nan to a bakin auren da za muyi, sannan kuma zan daina sonki kuma bazan kara neman aurenki ba har a abada kuma ko a ina kika ganni kar ki nuna kin sanni balantana ki min magana. yana zuwa dai dai nan ne mahaifiyarki ta fasa fita daga dakin. a dole ta dawo da baya ta zo ta kwanta a kan gadonsa tana kuka. tayi hakane don ta faranta masa rai kuma ita bata so ta rabu da shi domin kuwa inhar ta rabu da shi baza ta ba iya rayuwa a duniyar nan ba. idanuwan mahaifiyarki a rufe sannan tana kuka har mahaifinki yayi abun da yake so da ita ya gama. ha ta tashi ta tafi gida cikin bakin ciki da tashin hankali. amma da ta je kofar gidansu sai ta daina kuka sannan ta nutsu kamar babu abun da ya shiga tsakqninsu da mahaifinki. Bayan kwana hudu ne mahaifiyarki ta ringa amai, amma kuma bata yarda iyayenta sun gane aman da take ba saboda ta san halin da take fiki na samun juna biyu. Haka ta zo ta samu mahaifinki ta gaya masa sai ya ce to tunda babu wanda ya sani daga shi sai ita kawai suje asibiti a zubar da cikin. sai mahaifiyarki ta ce sam baza tq yarda a zubar da cikin ba saboda inahar ta amince anzubar da cikin to tamkar tayi kisan kai ne. da ya ji haka sai ya ce ai kuwa inhar bata yarda anzubar da cikin ba to bazai aure ta ba zai je ya samu iyqyensa a fasa auren. koda da mahaifiyarki ta ji haka sai ta fashe da kuka ta ce inhar kasanar musu a fasa auren dolesu tambayeka dalilin da yasa ka ce a fasa aure. to idan sun tambayeka dalilin fasa auren mi za ce musu? sai yayi shiru bai ce komai ba. sai ta kara cewa to dan haka ka bari ayi auren kawai mu rufawa junanmu asiri sannan mu tuba ga Allah bisa abun da muka aikata. shi kuwa yana jin haka sai ya ce sam bq yarda nq qureki ba sai kawai ya shige gida ya barta a nan tana kuka. a dole ta tashi ta tafi gida cikin kunci da bakin ciki. haka mahaifinki ya je gida ya ce ya fasa aurenki amma da aka tambaye shi dalili sai yayi shiru bai ce komai ba. sai iyayensa suka ce to baza a fasa aurenku ba. A dole ya hakura akayi auren, amma kuma ya dauki tsanar duniyar nan ya dorawa mahaifiyarki.. ....Allah sarki! wasu mazan kam saiMA ZAHRA novels / RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 12 RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 12 Posted by Bashir Sani Fesan on 27 Dec 2016 - 13:17 amma ya dauki tsanar duniyar nan ya dorawa mahaifiyarki. Mahaifiyarki ta fada cikin rayuwa mai kunci tare da fuskantar wulakanci a gun mahaifinki har cikin da take dauke da shi ya girma, sai ya zamana bata aiki yanda ya kamata. to shine a ka dauke ni mai aiki a gidanku ina shara da wanke wanke da kuma wanki. shi kuwa mahaifinki sai ya karo aure ya zamana amaryar babanki mai suna kaltume itama ta ringa hantarar mahaifiyarki ita da mahaifinki, tamkar wata baiwarsu. Duk abubuwan da suke faruwa ga mahaifiyarki bata taba fada a gidansu ba ko gidansu mijinta. sai dai duk lokacin da suka tambayeta babu matsala sai ta ce musu babu komai. Haka mahaifiyarki ta kasance cikin halin tausayawa, har ya kasance idan za tayi wani aiki sai na zo na karbe ta amma kuma idan amaryar babanki ta ga ina taimakawa mahaifiyarki sai ta zo ta zazzage ni ta kore ni sannan ta ce inhar ina taimaka mata za ta sa a kore ni na bar aiki a gidanku, a dole zan bar taimawa mahaifiyarki na bata aikin da na taimaka mata akai. Duk tausayawan da nake yiwa mahaifiyarki, sai ya zamana tausayinta da nayi a ranar da zata haifu ya ninka na baya. domin kuwa duk mutum mai imani idan ya ga halin da mahaifiyarki takasance a ranar da zata haifu dole ya ji tausayi mahaifiyarki. domin kuwa bana manta ranar juma"a da yamma mahaifiyarki tana kitchen ta dora ruwan tuwon dare sai nakuda ta kama a kitchen din ni kuma a lokacin ina waje ina shara. sai na jiyo mahaifiyarki tana cewa a taimaka min wayyo! cikina. cikin sauri na jefar da tsinshiyar da ke hannuna na ruga cikin kitchen din don na taimakawa mahaifiyarki. kafin na shiga kitchen din sai mahaifiyarki ta yanki jiki ta fadi tana nishi alamar haifuwa za tayi. koda na shiga sai na kwalla kiran amaryar babanki akan ta zo mu taimaka mata ashe ita tana cikin falo tana kallon tv. da naga bata zo ba sai na ruga a guje cikin falon ina cewa hajiya kaltume. koda na shiga falon sai naga tana kallon tv a kidimauce na sanar mata halin da mahaifiyarki take ciki.cikin harar tare da daka min tsawa ta ce to ina ruwanta da ita ta mutu man. koda na ji abun da amaryar babarki ta ce sai na juya cikin kitchen da nufin na je na taimaka mata. sai na ji amaryar babarki cikin tsawa ta ce min kina komawa cikin kitchen din nan a bakacin aikinki. haka a dole na fita waje na je na tsaya a kusan kitchen din ina kallon hallon halin da mahaifiyarki take ciki a lokacin sai hawaye suka kwararo daga idanuwana tsabar tausayin mahaifiyarki. ita kuwa mahaifiyarki sai nishi take tana kuka tana cewa kuzo ku taimake ni, ina jinta tana kiran sunana tana cewa ki taimaka min. tana cikin wannan halin nakuda ne amaryar babarki ta shiga kitchen din tana cin chew gum, sai ta je bakin kofar kitchen din ta tsaya tana yiwa mahaifiyarki dariya tana cewa sai dai ki mutu babu wanda zai taimaka min idan kinyi niyar haifuwa ki haifu idan kuma baza ki haifu ba ki mutu. haka mahaifiyarki ta ringa kuka tana nishi tare da juye juye har dan dake cikinta ya fara fitowa, haka ta cigaba da nishi tare da cizon bakinta har ta haifu. koda ta haifu sai jikinta ya sassake sai ta fara ambaton zata sha ruwa cikin sauri na debo ruwa a kofi na shiga kitchen din da gudu na je na durkusa a gabanta na tallafo kanta zan bata ruwan. sai na ji amaryar banki ta doke kofin sannan ta gaura min mari ta ce shegiya tsinanniya ba na ce karki sake ki shigo kitchen din nan ba amma sai da ki ka shigo. amaryar babanki tana cikin gaya min haka sai naga mahaifiyarki ta dakko dan da ta haifa cikin jini shi kuma jaririn sai kuka yake. ko cibiya ba a yanke ba mahaifiyarki ta dora jaririn a kirjinta ina ji tana kuka kana cewa ya Allah kai kasan abun da na haifa amma ni ban sani ba ya Allah ga amana ta nan a gareka ka kare min abun da na haifa domin kuwa mutuwa zanyi sai ta kara kankame jaririn da ta haifa sannan ta ce jaririna gashi kazo cikin duniya cikin wani irin yanayi da wahala amma gashi zan mutu na barka, sai na ji tayi wani irin jan numfashi sannan ta fara kalmar shahada can sai naji ta ja dogon numfashi sannan jikinta ya mike alamar fitar rai, sai kuma na ga jikinta ya sandare. ashe Allah ya mata cikawa. [10:40AM, 5/11/2015] Asmeer: ita amaryar babanki a lokacin bata san mahaifiyaki ta rasu ba, ko imani babu ta dakko wuka ta yake cibiyar jaririyar da mahaifiyarki ta haifa sannan ta fizgi jaririn a hannun mahaifiyaki tana fizgar dan kuwa sai hannayen mahaifiyarki suka fadi kas sharaf.. sai kuma amaryar baban naki tace to munafuka sai ki tashi ki karbi jariri yar taki. ita a tunaninta mahaifiyarki bata mutu ba saboda ta ga idanuwanta a kafe.shi kuwa jaririn sai rusa kuka yake ko wanke jinin da ke jikinsa ba ayi ba balantana a lullubeshi a cikin tawul. ni kuwa koda naga haka sai na fashe da kuka sannann na matsa kusa da gawar mahaifiyarki na shafe mata idanuwanta ina cewa Allah ya ji kanki ya gafarta miki yasa iyakar wahalarki ke nan. ita kuwa amaryar babanki tsabar jahilci sai take cewa au dan na ce ki tashi shine kika yi barci ko? sai ta ce min ke kuma tsinanniya har da wani cewa Allah ya ji kanta ai ba mutuwa tayi ba. ni dai shiru nayi ina ta kuka ban ce mata komai ba. A dai dai lokacin ne muka ji shigowar motar mahaifinki. ai kuwa da sauri amaryar babarki ta a jiye jaririn a kas tafita a kitchen din ta doshi hanayar zuwa wajen mahaifinki ni kuma sai na dauki jaririn a hannuna ina kuka sai a lokacin na lura ashe mace ce mahaifiyarki ta haifa kuma wannan jaririyar ke ce. Bayan amaryar babanki ta je ta gaya masa abun mamaki sai naga ya shigo kitchen da sauri.koda ya zo ya taras da mahaifiyarki a kwance cikin jini ga kuma idanuwanta a rufe sai jikinsa yayi sanyi sai ya sunkuya a gaban mahaifiyarki yana cewa bacci take yi ne cikin halin damuwa na ce masa a"a ai Allah ya mata rasuwa sai naga wani gumi ya keto masa sai ya daga hannun mahaifiyarki sai ya sake sai ya ga ya fadi sharaf. sai kawai na ga idanuwansa sun fara zubar da kwalla. tun daga lokacin ya fara dana sanin abubuwan da yayiwa mahaifiyarki. da amaryar babanki ta ga mahaifinki na zubar da hawaye sai ta ce akan jakar nan kake kuka. cikin fushi ya mike ya zabga mata mari ya ce ke wace irin marar imani ce kina ganin a yanayin da fatima ta rasu zaki ki ce mata jaka. ki fice a cikin kitchen din nan ko ranki ya baci. koda ta ji cewa mahaifiyarki ta mutu ko dar ba ta ji ba sai kawai take cewa mahaifinki akan wannan la"ananniyar zaka mare ni to ai mutuwarta abun farin ciki ne a gare mu. hannu ya kara dagawa zai kara zabga mata mari amma sai ya fasa ya ce bana ce ki fita ba. cikin fushi ta fita tana cewa ai zaka zo ka same ni. ke kuwa kina hannuna kina kuka, sai mahaifinki ya ce na dauke ki na je na wanke ki sannan na je na samu abun da zan lullube ki. sai na tashi na je na debi ruwan da mahaifiyarki ta dora na je na wanke ki da shi, sannan na je na shiga dakin mahaifiyarki don neman abun da zan lullube shi da ke. shi kuwa mahaifinki waya ya dakko ya kira mahaifyar mamanki ta zo tayi koke kokenta sannan aka yiwa mahaifiyarki wanka aka mata sutura sannan aka taro jama"a aka yi mata salla aka kaita kushewarta. Bayan na shiga dakin mahaifiyarki ne tausayin mahaifiyarki ya kara kamani sai da na kara zubar da hawaye domin kuwa abubuwan da mahaifiyarki ta tanadawa jaririn da zata haifa. kaya ne na jarirai da kayan mata da na maza ga kuma duk wasu abubuwan da ake siya don tanadi ga abun da za a haifa. sai dai kuma kash mahaifiyarki bata ga ranar da za tayi amfani da wadannan kayayyaki ba...... ....pls kumin afuwa bisa dakatawa da nayi a nan. hawaye ne ke zuba daga idanuna sannan na gagara cigaba da typing bisa tsantsar tausayin da ya kamani.IMA ZAHRA novels / RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 13 RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 13 Posted by Bashir Sani Fesan on 27 Dec 2016 - 13:22 amma kuma kash! mahaifiyarki bata ga ranar da za tayi amfani da kayayyakin ba. ka fin a nemo wanda za ta ringa shayar da ke ni da kaina nake baki madara a fida, sannan kuma a nan gidanku nake kwana a dakin mahaifiyarki tare da ke, saboda ina baki kulawa. Bayan an gama.zaman makokin mahaifiyarki da sati daya ne sai aka yi radin sunanki aka yanka miki rago sai mahaifinki ya ce a na kiranki da suna fatima Zahra saboda yana tunowa da mahaifiyarki. bayan kwana uku da radin sunanki sai amaryar babarki mahaifinki ta same shi take ce masa ita fa a gaskiya baza ta iya zama da ke ba saboda ta tsaneki. shi kuwa ya ce to ina zai kai ki to? sai amaryar babarki ta ce ita fa a gaskiya baza ta cigaba da kallonki ba saboda inhar tana kallonki tamkar mahaifiyarki take kallon. sai kawai ta ce kashe ki shi yafi mata sauki da kwanciyar hankali. Tabbas babu shakka amaryar babanki asiri ta yiwa mahaifinki, domin kuwa lokacin da ta ce a kashe ki sai yayi shiru sannan ya ce to ta yaya za a kashe ki ba tare da mutane sun gane kashe ki aka yi ba? sai amaryar banbanki ta ce abu mai sauki shine ya dauke ki da daddare ya je ya toni rami a bayan gari ya binneki kawai. jikin mahaifinki yana rawa a dole yazo ya same ni a dankin mahaifiyarki yanda muke kwana da ke, yazo ya ce min na bashi ke tare yake so ku kwana. koda na ji abun da ya ce sai jikina yayi sanyi sannan na ji cewa to ke da kike jaririya kuma mai son samun kulawa daga hannun mai shayar da ke to shi mahaifinki mi yasa ya ce zai kwana da ke alhalin bai taba kwana da ke ba bugu da kari amaryar banbanki ta tsane ki shin tasan mahaifinki zai kwana da ke kuwa? haka dai na bashi ke a lokacin kuwa sai barci kike yi, bayan na bayar da ke ga mahaifinki sai na bishi a baya don na tabbatar da abun da ya fada min. ina biye da shi a baya sai na ga sun tsaya da amaryar babanki a tsakar gida tana masa bayani yanda zai tuni rami ya sakaki da kuma wajen da zai je ya binneki. bayan ta gama masa bayani sai ta mika masa fartanya ya karba ya shiga mota ya tafi da ke. jikina yana rawa na je na dauki hijab dina na bishi a baya. ina fita waje kuwa nayi sa"ar samun dan a caba da yake dare bai yi sosai ba. sai na cewa dan a can ya bi bayan motar babanki. sai ya bishi a baya duk inda mahaifinki yayi muna biye da shi. bayan munyi tafiya mai nisa sai na ga mahaifinki ya tsaya da motarsa a can bayan gari. koda na ga ya tsaya sai na umarci mai mashin din ya tsaya nesa da shi, sai mai a caban ya tsaya a dai dai wajen da zan ringa hangowa duk abun da mahaifinki zai yi. sannan dan a caban ya kashe fitillar mashin nasa. amma kuma mahaifinki bai kashe fitillar motarsa ba saboda tana haska masa duk abun da zai yi. muna can daga nesa ni da dan a caba sai muka hango shi yana tonan rami bayan ya gaba sai ya dakkoki zai saka ki. amma abun mamaki sai ya fasa ya dauki lokaci mai tsawo yana rike da ke a hannunsa ya garara sakaki a ramin. can sai mu ka ga ya fasa sakaki a ramin yana zubar da hawaye. sai ya dauke ki ya miyas da ke cikin motar sannan ya shiga yayi key a motar ya bar wajen. maimakon yayi hanyar gida sai na ga yayi wata hanya dabam. cikin sauri na cewa dan a caban yayi sauri ya bi bayansa. cikin gaggawa dan a caban ya kara bin bayan motar mahaifinki. mun kara tafiya mai nisa sai na ga mahaifinki ya shiga gidan marayu da ke. bayan ya shiga gidan marayun da ke sai na cewa dan a caban ya tsaya da ni a bakin kofar gidan marayun zan shiga na ji mi zai ce musu. sai na sauka a mashin din na shiga cikin gidan marayun. ina shiga kuwa sai mai gadi ya tsayar da ni ya ce ina zan je? sai na ce na zo zan taimakawa marayu ne. da yake an biyani albashin aikina da nake yi a gidanku. sai na bude jakata na ciro dari biyu na bawa mai gadin cikin murna tare da cewa aaa babu komai hajiya shiga kawai Allah ya bada lada. kai tsaye na shiga ciki, ina shiga kuwa na hango mahaifinki har ya dakkoki ya nufin shiga wajen da ake register na karban marayu. haka da na bi bayansa a hankali har muka shiga wajen register . muna shiga kuwa na tsaya a bakin kofa ban karisa ciki ba. Bayan ya shiga har sun gaisa da manajan office din sai na ji yana cewa manajan wannan jaririyar "yata ce mahaifiyarta ta rasu a wajen haifuwarta. sannan kuma mun nemin wacce zata shayar da ita ba mu samu ba shine na dakkota na kawo ta nan don ana bata kulawa. sai manajan ya ce eh zamu karbeta amma sai da dan sanda da kuma shedu uku. sai mahaifinki ya ringa bashi hakuri da ya karbeki domin kuwa yanzu dare yayi ba zai iya samowa abun da ya gaya masa ba. [11:04AM, 5/12/2015] Asmeer: Haka dai manajan ya karbe ki sannan ya mikawa mahaifinki wata takarda ya ce ya cika takardar sannan yasa hannu. bayan ya cika sai yasa hannun. bayan sun gama sai nayi sauri na fito na hau mashin din dan a caban da muka zo da shi. bayan mun karso kofar gida na dauki dubu daya na bawa dan a caba. yayi min godiya ya tafi. shi kuwa mahaifinki bayan ya dawo gida sai yayiwa amaryar babanki karyar cewa ya je ya binneki, har ya binneki ba wanda ya ganshi. murna tayi sosai har da cewa yauwa sai yanzu na ji sanyi a raina yanzu babu wata matsala tattare da shi. Haka amaryar babanki ta kasance da mahaifinki tana juya shi yanda taso. sai abun da tace yayi yake yi. sai da ya zamto ta rabashi da "yan uwansa bisa taimakon malamin da take zuwa wajensa. ni kuma bayan wata daya da kaiki gidan marayu sai nayi aure, amma bayan nayi aure da wata biyu na dawo gidanku na cigaba da aikina. saboda mijina mai karamin karfi ne. Amma kuma ita amaryar babanki bata taba haifuwa ba, sai abun ya fara damunta sai ta samu mahaifinki cikin masifa ta ce ita fa ta ga ji da rashin haifuwa. shi kuwa mahaifinki ya ce ai matsalar ba a gunsa ba ne a gunta ne tunda ya haifu da mahaifiyarki, amma haka taki ta ce sam bata yarda ba matsalar a gunsa ne dan haka su je asibiti a gwada su. haka kuwa aka yi suka je asibiti aka gwada su sai aka samu matsalar a wajenta ne. haka dai amaryar babanki tq hakura ta cigaba da zama da mahaifinki har suka kai shekara bakwai. sai kawai amaryar babanki ta tayar da bori ita fa haifuwa take so. amma sai mahaifinki ya ce to ya zai yi sai dai idan zai karo aure. ai kuwa tana jin haka sai ta ce to ta fasa son haifuwar amma dai duk inda zai yi ya samo mata da koda kuwa gidan marayu zai je ya samo toya je. koda mahaifinki ya ji haka sai yayi murna sosai. sai kawai ya je gidan marayun da ya kai ki ya dakkoki. Ai kuwa yana shigowa da ke cikin gidan jikina ya ban ke ce FATIMA ZAHRA "yar marigayiya FATIMA ZAHRA saboda kuwa kamar ku daya tamkar an tsaga kara duk abun da mahaifiyarki take da shi kina da shi har tsayinta ma shi kika dakko ga yalwantar gashi har gadon baya. ina ganinki kuwa na cika da farin ciki domin kuwa kin dawo gidan mahaifinki sannan kuma kullum kewarki da nake yi ga shi kin dawo Ita kuwa amaryar babanki da ta ganki sai tayi murna sosai. amma kuma ko kula da kamar da kuke yi da mahaifiyarki ba tayi ba. Tun daga ranar da aka kawo ki ni take miki wanka na miki kwalliya sannan kuma na saka miki kaya. Mahaifinki kuwa yana mutukar sonki nesa ba kusa ba duk sanda ya dawo daga wajen aikinsa sai ya siyo miki abun da zai faranta miki. bayan sati daya ne ya sakaki a makaranta. da kansa yake kaiki makaranta. ita kuwa amaryar babanki tana sonki amma ba kamar mahaifinki ba. akwai watarana da safe bayan na saka miki kayan makarantarki. kin fito za ku tafi da mahaifinki, daman kuwa kullum kafin ki tafi makaranta zaki je ki gaisar da amaryar babanki wacce kika dauka ita ce mahaifiyarki. bayan kin fito zaku tafi sai kika taras da amaryar babanki a falo a zaune. bayan kin durkusa a gabanta kin gaishe ta. ai kuwa sai amaryar babanki da lura da kamannin da kuke da mahaifiyarki. sai kawai ta ji kirjinta ya buga da] Asmeer: <<>>Part 14 ...sai kirjinta ya buga da karfi. bata ce komai ba sai kawai ta biki ta kallo har kuka fita a gidan ke da mahaifinki. Bayan fitarku ne ta je ta shiga dakinta ta ringa sake sake a kanki,amma ban san mi take sakawa ba a kanki. To da yamma bayan kin dawo har kin tafi islamiyya. ina jin amaryar babanki tana cewa mahaifinki mai gida na ga dawainiyar da kake yi na kaiwa "yar da ka kawo mana na kai ta makaranta ya maka yawa, shin da wanne za ka ji da kaita makaranta ko da zuwa wajen aikinka? sai kawai yayi murmushi ya ce amaryata ke nan ai ba abun wahala ba ne don ina hidima ga "yar da na haifa. cikin zare ido ta ce "yar ka kuma? wacce "yar ke nan? sai kawai mahaifinki yayi ajiyar zuciya sai ya kara murmushi ya ce ba haka nake nufi ba. ina nufin ai "yar da muka dakko tamkar "yar da muka haifa ne kuma ni da ke munyi alkawarin za mu rike ta tamakar "yar da muka haifa. wani irin kallo amaryar babanki ta yi masa sai ta ce eh haka ne kam, amma kuma na ga kamar suna kama da marigayi kishiyata fatima. A razane maihaifinki ya ce to miki ke nufi da haka? sai ta tuntsure da dariya ta ce eh naga komai na wannan "yar da ka kawo tamkar na marigayiya ne hatta tafiyar ma irin na ta ce, anya kuwa wannan "yar da ka kawo ba ita ba ce fatima "yar marigayiya ba?. murmushi kawai yayi ya ce ya zaki ce haka alhalin ke kika ce min na je na binneta a can bayan gari. wani irin kallo ta kara masa tare da wani irin murmushi mai dauke da ayar tambaya sai ta kara ce masa hmmm.. anya kuwa ka binneta, ni kam jikina yana ban wannan "yar da ka kawo min ita ce fatima. wani irin gumi ne ya ketowa mahaifinki cikin kame kame ya ce ke banda abunki ina kika taba ganin an bunne abu mai rai har na tsawon shekara bakwai amma ya fito da ransa? sai ta ce na sani ko a lokacin da ka je binneta fasawa kayi ka kaita wani waje na daban. sannan yanzu ka dawo da ita. cikin hada fuska ya ce look i dnt like this kind of jokes, ya za ayi nayi wani abu na dabam game da abun da kika ce nayi. murmushi kawai ta yi ta ce to shi ke nan na ji ka yi duk abun da na ce kayi, amma abun da nake so da kai shine tunda nima tamkar uwa nake a gunta kuma ina sonta ina son ka barni ina kaita makaranta ina dawowa da ita. sai babanki ya ce hmmm dama kin bari ina kaita tunda ina da mota ke kuwa nasan a mashin zaki ringa kaita ko a cikin a daidaita sahu(keke napep). sai kawai ta bata rai ta ce ka nuna min ni ba "yata ba ce kuma bani da iko a kanta ko? cikin rarrashi jikinsa a sanyaye ya ce haba! amaryata ta kaina miye kuma na yin fushi? to kin kwantar da hankalinki ke za ki ringa kaita kullum. cikin murna ta ce yauwa har na ji dadi. sai ya kara cewa dan haka zan sama muku mai keke napep din da zai ringa kaiku kullum kuna dawowa. sai ta ce yauwa hakan ma yayi. sai ya tashi ya ce bari ma na je na samu dan makwabtanmu lawwali mai keke napep, na gaya masa daga gobe yazo yana kaiku. ita kuwa a maryar babanki bin mahaifinki tayi da kallo tana cizon le6enta tana cewa ashe daman baka kashe ta ba kazo ka ce min ka kasheta ko? hmmm, ukubar da zan ringa zabga mata har sai yayi sanadiyar mutuwarta. a haka dai har haifinki ya fita. kashe gari da safe sai ga lawwali mai keke napep yazo daukansu. a lokacin kuwa na gama miki shirin makarantarki sai na fito da ke cikin falo sai na taras da mahaifinki ya gama shirinsa na tafiya office, ita kuwa amaryar babanki tana zaune kusa da shi. bayan mun kariso wajensu sai muka durkusa a gabansu muka gaida su. wani irin kallo amaryar babanki ta yi min sannan ta ce min Maryam daga yau ni zan ringa yiwa "yar mun nan wanka da sauran kulawa. na budi baki zanyi magana sai mahaifinki ya ce nayi shiru kar na ce komai abun da amarya ta fada shi za a ringa yi. sai ya kalli a maryar ya ce to ku tashi ku tafi tun dazu lawwali ya zo yana jiranku a wa je. sai kawai amaryar babanki ta dauki gyalenta ta yafa sannan ta kama hannunki kuka fita waje da nufin kai ki makaranta. shima mahaifinki mikewa yayi dauke da jakarsa ta zuwa office ya bi bayanku ya je ya shiga motarsa ya tafi office. [10:09AM, 5/14/2015] Asmeer: Abun da mai wuce minti goma da fitarku da amaryar babanki ba sai na ga ta shigo cikin falon rike da ke kina kuka. sai kawai jikina ya ban akwai abun da amaryar babanki take nufi da ke na mugunta. ina ganinku tare sai nayi sauri na bar sharan da nake yi a cikin falon na nufi dakina. cikin sauri ta daka min tsawa ta ce munafuka ina zaki je ki kuma? daga ganinmu zaki tafi daki. cikin sanyin jiki na tsaya kaina a sunkuye ban ce mata komai ba. sai ta matso kusa da ni. duk da na fita yawan shekaru amma ko kunya bata ji ba ta kama kunnena sai kace karamar yarinya ta ce min kar ki ga na dawo da wannan tsinanniyar "yar daga makaranta ki budi bakinki ki gayawa mijina, inhar kika gaya masa barin aikin gidan nan za kiyi sannan kuma na wulakanta ki. duk abun da kika ga ina yi mata ki ja bakinki ki shiru, sai ta jijjiga kunnena ta ce kinji ko baki ji ba? kaina na girgiza na ce na ji. sai ta sau min kunnena sannan ta ce to maza je ki cigaba da aikinki. aikina na je na cigaba da yi ko daga kaina na kalleta ban yi ba. tabbas! ba dan ina samun abun da zamu ci da mijina ba da kuma albashin da nake dauka a gidan mahaifinki ba don rufawa kaina asiri ba, da tuni na bar aikin gidanku. sannan bugu da kari ina sonki da kuma tausaya miki halin da kike ciki da bazan zauna ba. ke kuwa halin tausayawa da wahala kika fada a hannun amaryar babanki. domin kuwa idan amaryar babanki ta dauke ki da nufin kaiki makaranta idan kunje bakin makarantar sai ku hau mashin ku dawo gida. sannan amaryar babanki ta dora miki talle ki tafi, sannan sai ta gargade ki kar ki sake ki gayawa mahaifinki, inhar kika sake kika gaya masa sai ta kashe ki. haka zaki ki ki gayawa mahaifinki inhar ya tambayeki akwai wata damuwa sai kawai ki ce a"a babu. akwai watarana kin dawo daga tallen da kike yiwa a maryar babanki sai ta kamaki ta ce zata miki wanka kina doyi, sai kawai ta tafasa ruwan zafi ta ringa watsa miki da kofi. kina kuka kina cewa mama ruwan da zafi amma haka zata ringa dukanki tana cewa dan uwarki idan ba ruwa mai zafi na wanke ki da shi ba baza ki daina doyi ba. "kai gaskiya amaryar babanki bata da imani domin kuwa a ranar ina kallo tana miki wannan ukubar sai da na zubar da hawaye." sannan kuma bayan ta gama miki wanka da ruwan zafin sai ta dakko abinci mai zafi wanda ita ta dafa miki don ta azabatar da ke. haka abincin yana tiriri ta kawo miki gabanki ta ce ki ci kina kuka kina cewa mama abincin fa da zafi. sai ta gaura miki mari ta ce ai sai kinci abincin nan idan ba haka ba yau na yankaki daman na tsanki tun lokacin da na gane ke "yar kishiyata ce. dan haka daga yau karki kara kira na da mama, saboda ni ba uwarki ba ce. sai ta daka miki tsawa ta ce saka hannunki ki ci ko na dura miki da karfi da ya ji. kina kuka sannan jikinki na rawa kika saka hannu zaki debi abincin, kina sakawa kuwa kika cire kina cewa da zafi sai kawai shiga kitchen ta dakko chokali sannan ta danneki tana cewa shegiya "yar ala tsine sai kinci kina ihu kina kuka tana dura miki. tsabar azaba da gigicewa sai ta kika suma. koda ta ga kin baje a kasa baki motsi sai ta dagagi tana dariyar mugunta tana cewa shegida har bacci tayi tsabar wahala. sai kuma ta fara taba ki tana cewa tashi ki karisa abincin, koda ta daga hannunki da nufin tayar da ke sai ta ga hanunki ya fadi sharaf..sai kawai ta kara tuntsurewa da dariya tana cewa shigiya ta mutu. Ni kuwa kuka na ringa yi tamkar a ni ake yiwa abun da ake miki. koda na ji tana cewa kin mutu sai na ji gaina ya fara wani matsakaicin ciwo sannan na fara jin hajijiya... ...kai! mata wannan wani irin kishi ne] Asmeer: <<>>Part 14 ...sai kirjinta ya buga da karfi. bata ce komai ba sai kawai ta biki ta kallo har kuka fita a gidan ke da mahaifinki. Bayan fitarku ne ta je ta shiga dakinta ta ringa sake sake a kanki,amma ban san mi take sakawa ba a kanki. To da yamma bayan kin dawo har kin tafi islamiyya. ina jin amaryar babanki tana cewa mahaifinki mai gida na ga dawainiyar da kake yi na kaiwa "yar da ka kawo mana na kai ta makaranta ya maka yawa, shin da wanne za ka ji da kaita makaranta ko da zuwa wajen aikinka? sai kawai yayi murmushi ya ce amaryata ke nan ai ba abun wahala ba ne don ina hidima ga "yar da na haifa. cikin zare ido ta ce "yar ka kuma? wacce "yar ke nan? sai kawai mahaifinki yayi ajiyar zuciya sai ya kara murmushi ya ce ba haka nake nufi ba. ina nufin ai "yar da muka dakko tamkar "yar da muka haifa ne kuma ni da ke munyi alkawarin za mu rike ta tamakar "yar da muka haifa. wani irin kallo amaryar babanki ta yi masa sai ta ce eh haka ne kam, amma kuma na ga kamar suna kama da marigayi kishiyata fatima. A razane maihaifinki ya ce to miki ke nufi da haka? sai ta tuntsure da dariya ta ce eh naga komai na wannan "yar da ka kawo tamkar na marigayiya ne hatta tafiyar ma irin na ta ce, anya kuwa wannan "yar da ka kawo ba ita ba ce fatima "yar marigayiya ba?. murmushi kawai yayi ya ce ya zaki ce haka alhalin ke kika ce min na je na binneta a can bayan gari. wani irin kallo ta kara masa tare da wani irin murmushi mai dauke da ayar tambaya sai ta kara ce masa hmmm.. anya kuwa ka binneta, ni kam jikina yana ban wannan "yar da ka kawo min ita ce fatima. wani irin gumi ne ya ketowa mahaifinki cikin kame kame ya ce ke banda abunki ina kika taba ganin an bunne abu mai rai har na tsawon shekara bakwai amma ya fito da ransa? sai ta ce na sani ko a lokacin da ka je binneta fasawa kayi ka kaita wani waje na daban. sannan yanzu ka dawo da ita. cikin hada fuska ya ce look i dnt like this kind of jokes, ya za ayi nayi wani abu na dabam game da abun da kika ce nayi. murmushi kawai ta yi ta ce to shi ke nan na ji ka yi duk abun da na ce kayi, amma abun da nake so da kai shine tunda nima tamkar uwa nake a gunta kuma ina sonta ina son ka barni ina kaita makaranta ina dawowa da ita. sai babanki ya ce hmmm dama kin bari ina kaita tunda ina da mota ke kuwa nasan a mashin zaki ringa kaita ko a cikin a daidaita sahu(keke napep). sai kawai ta bata rai ta ce ka nuna min ni ba "yata ba ce kuma bani da iko a kanta ko? cikin rarrashi jikinsa a sanyaye ya ce haba! amaryata ta kaina miye kuma na yin fushi? to kin kwantar da hankalinki ke za ki ringa kaita kullum. cikin murna ta ce yauwa har na ji dadi. sai ya kara cewa dan haka zan sama muku mai keke napep din da zai ringa kaiku kullum kuna dawowa. sai ta ce yauwa hakan ma yayi. sai ya tashi ya ce bari ma na je na samu dan makwabtanmu lawwali mai keke napep, na gaya masa daga gobe yazo yana kaiku. ita kuwa a maryar babanki bin mahaifinki tayi da kallo tana cizon le6enta tana cewa ashe daman baka kashe ta ba kazo ka ce min ka kasheta ko? hmmm, ukubar da zan ringa zabga mata har sai yayi sanadiyar mutuwarta. a haka dai har haifinki ya fita. kashe gari da safe sai ga lawwali mai keke napep yazo daukansu. a lokacin kuwa na gama miki shirin makarantarki sai na fito da ke cikin falo sai na taras da mahaifinki ya gama shirinsa na tafiya office, ita kuwa amaryar babanki tana zaune kusa da shi. bayan mun kariso wajensu sai muka durkusa a gabansu muka gaida su. wani irin kallo amaryar babanki ta yi min sannan ta ce min Maryam daga yau ni zan ringa yiwa "yar mun nan wanka da sauran kulawa. na budi baki zanyi magana sai mahaifinki ya ce nayi shiru kar na ce komai abun da amarya ta fada shi za a ringa yi. sai ya kalli a maryar ya ce to ku tashi ku tafi tun dazu lawwali ya zo yana jiranku a wa je. sai kawai amaryar babanki ta dauki gyalenta ta yafa sannan ta kama hannunki kuka fita waje da nufin kai ki makaranta. shima mahaifinki mikewa yayi dauke da jakarsa ta zuwa office ya bi bayanku ya je ya shiga motarsa ya tafi office. [10:09AM, 5/14/2015] Asmeer: Abun da mai wuce minti goma da fitarku da amaryar babanki ba sai na ga ta shigo cikin falon rike da ke kina kuka. sai kawai jikina ya ban akwai abun da amaryar babanki take nufi da ke na mugunta. ina ganinku tare sai nayi sauri na bar sharan da nake yi a cikin falon na nufi dakina. cikin sauri ta daka min tsawa ta ce munafuka ina zaki je ki kuma? daga ganinmu zaki tafi daki. cikin sanyin jiki na tsaya kaina a sunkuye ban ce mata komai ba. sai ta matso kusa da ni. duk da na fita yawan shekaru amma ko kunya bata ji ba ta kama kunnena sai kace karamar yarinya ta ce min kar ki ga na dawo da wannan tsinanniyar "yar daga makaranta ki budi bakinki ki gayawa mijina, inhar kika gaya masa barin aikin gidan nan za kiyi sannan kuma na wulakanta ki. duk abun da kika ga ina yi mata ki ja bakinki ki shiru, sai ta jijjiga kunnena ta ce kinji ko baki ji ba? kaina na girgiza na ce na ji. sai ta sau min kunnena sannan ta ce to maza je ki cigaba da aikinki. aikina na je na cigaba da yi ko daga kaina na kalleta ban yi ba. tabbas! ba dan ina samun abun da zamu ci da mijina ba da kuma albashin da nake dauka a gidan mahaifinki ba don rufawa kaina asiri ba, da tuni na bar aikin gidanku. sannan bugu da kari ina sonki da kuma tausaya miki halin da kike ciki da bazan zauna ba. ke kuwa halin tausayawa da wahala kika fada a hannun amaryar babanki. domin kuwa idan amaryar babanki ta dauke ki da nufin kaiki makaranta idan kunje bakin makarantar sai ku hau mashin ku dawo gida. sannan amaryar babanki ta dora miki talle ki tafi, sannan sai ta gargade ki kar ki sake ki gayawa mahaifinki, inhar kika sake kika gaya masa sai ta kashe ki. haka zaki ki ki gayawa mahaifinki inhar ya tambayeki akwai wata damuwa sai kawai ki ce a"a babu. akwai watarana kin dawo daga tallen da kike yiwa a maryar babanki sai ta kamaki ta ce zata miki wanka kina doyi, sai kawai ta tafasa ruwan zafi ta ringa watsa miki da kofi. kina kuka kina cewa mama ruwan da zafi amma haka zata ringa dukanki tana cewa dan uwarki idan ba ruwa mai zafi na wanke ki da shi ba baza ki daina doyi ba. "kai gaskiya amaryar babanki bata da imani domin kuwa a ranar ina kallo tana miki wannan ukubar sai da na zubar da hawaye." sannan kuma bayan ta gama miki wanka da ruwan zafin sai ta dakko abinci mai zafi wanda ita ta dafa miki don ta azabatar da ke. haka abincin yana tiriri ta kawo miki gabanki ta ce ki ci kina kuka kina cewa mama abincin fa da zafi. sai ta gaura miki mari ta ce ai sai kinci abincin nan idan ba haka ba yau na yankaki daman na tsanki tun lokacin da na gane ke "yar kishiyata ce. dan haka daga yau karki kara kira na da mama, saboda ni ba uwarki ba ce. sai ta daka miki tsawa ta ce saka hannunki ki ci ko na dura miki da karfi da ya ji. kina kuka sannan jikinki na rawa kika saka hannu zaki debi abincin, kina sakawa kuwa kika cire kina cewa da zafi sai kawai shiga kitchen ta dakko chokali sannan ta danneki tana cewa shegiya "yar ala tsine sai kinci kina ihu kina kuka tana dura miki. tsabar azaba da gigicewa sai ta kika suma. koda ta ga kin baje a kasa baki motsi sai ta dagagi tana dariyar mugunta tana cewa shegida har bacci tayi tsabar wahala. sai kuma ta fara taba ki tana cewa tashi ki karisa abincin, koda ta daga hannunki da nufin tayar da ke sai ta ga hanunki ya fadi sharaf..sai kawai ta kara tuntsurewa da dariya tana cewa shigiya ta mutu. Ni kuwa kuka na ringa yi tamkar a ni ake yiwa abun da ake miki. koda na ji tana cewa kin mutu sai na ji gaina ya fara wani matsakaicin ciwo sannan na fara jin hajijiya... ...kai! mata wannan wani irin kishi neOOKS [8:35AM, 5/16/2015] Asmeer: <<>>Part 15 ...sannan na fara jin hajijiya. amaryar babanki kuwa a tunaninta kin mutu don haka sai ta dakko waya ta kira mahaifinki tana kukan munafurci tana cewa masa "yar mu ta mutu kayi sauri ka dawo. cikin gaggawa sai ga mahaifinki ya dawo. zuwa yayi ya taras da ni a tsakar gida na durkusa kas ina kuka. kallona kawai yayi ya shige cikin falo da sauri yana zuwa kuwa ya taras da amaryarsa a gabanki tana kuka. cikin gaggawa ya tsugunna a gabanki "da yake shi ma"aikacin asibiti ne kuma shi Nurse ne" dan haka yana durkusawa sai ya daga hannunki yayi dube dube irin nasu na nurse, har kirjinki ya daba ko zai ji zuciyarki na bugawa, sannan ya bude idanuwanki. bayan ya gama dube dubensa sai ya ga kuma duk jikinki ya kumbura ga kuma bakinki yayi wani iri halamar dai ruwan zafi ya taba jikinki. jikinsa a sanyaye ya cewa amaryarsa ta debo masa ruwa. bata ce masa komai ba jikinta duk yayi sanyi sai ta je ta debo. bayan ta kawo masa sai ya yayyafa miki. ai kuwa yana yayyafa miki kika ja wani dogon numfashi sannan kika bude ido. bude idonki ke da wuya cikin kuka kika mike kika rungumi babanki kina kuka. ita kuwa amaryar babanki sai ta fara zare idanu tana muzurai. ganin yanda kika ta shi ne amaryar babanki jikinta ya fara rawa. saboda tana tsoron kar ki fadawa babanki abubuwan da ta miki. Babanki kuwa rarrashinki ya ringa yi har kika daina kuka, bayan kinyi shiru ne ya ke tambayarki mi ya same ki? bude baki kika yi za kiyi magana sai amaryar babanki tayi wuf...ta ce ta je zata dauki ruwan zafi a kitchen ne sai ruwan zafin ya zubo mata. sai babanki ya ce to bakinta fa mi yasa meshi haka ya kumbura? cikin kame kame ta ce eh shi kuma abinci take ci mai zafi sai ta ke kona bakinta. har nake cewa tayi a hankali. mahaifinki murmushi yayi ya ce hmmm...ita bata da rai ne take cin abincin da yake kona mata baki ba tare da ta daina cin abincin ba? shiru tayi bata ce masa komai ba. sai ya kalleki ya ce uwata ki gaya min gaskiyar duk abun da ya faru. bude baki ki kayi za kiyi magana sai amaryar babanki ta daka miki harara. shiru kika yi baki ce komai ba kika sunkuyar da kanki. da babanki ya ga haka sai ya lura da hararar da amaryarsa ta miki sai ya ce tabbas akwai abubuwan da kika yiwa wannan yarinyar. cikin masifa amaryar babanki ta mike ta ce kai! koma miye na yi sai mi? sai kawai ta doshi dakinta tana masifa. ni kuwa ina daga waje ina jin duk abun da suke yi, har a lokacin kuwa kuka na ke yi saboda nasan duk abun da ya faru tsakaniki da amaryar babanki. amma da yake amaryar babanki ta gargade ni da shiga sha"anin ta da ke. goge hawayen da ke zuba a idona nayi sannan na cigaba da shara. Mahaifinki kuwa daukanki yayi ya tafi da ke asibitin da yake aiki don duba lafiyarki. Bayan an gama dubaki aka rubuta miki magunguna sai ya dawo dake gida ya kwantar da ke a cikin dakinsa sannan ya kirani ya ce ina kula da ke shi zai koma asibiti don cigaba da aikinsa. haka na zo na zauna kusa da ke ina miki fifita. Tun daga wannan ranar kuwa mahaifinki ya daina tsoron amaryarsa sannan ya daina aikata duk abun da take so. sai ya zamana babu daidaituwa a tsakaninsu. sai ya zamana ya dora miki so da kauna a kanki tare da kulawa. sannan ya fara kewar mahaifiyarki. domin kuwa duk sanda ya zauna shi kadai sai yayi ta kuka bisa abubuwan da yayiwa mahaifiyarki, kusan kullum sai ya je kabarin mahaifiyarki ya ne mi tubarta sannan ya mata addu"ar samun rahma daga ALLAH. ita kuwa Amaryar babanki cikin bakin ciki ta fada ganin yanda mahaifinki ya canza, babu shiri ta tafi wajen malaminta wanda yake mata aiki ta sheda masa duk abubuwan da suke faruwa. sai malaminta ya yi wani zane zane a kas. sannan ya dago da kansa ya sheda mata cewa gaskiya mahaifinki yanzu yana kare kansa da addu"o"i dan haka sai dai tayi hakuri. cikin masifa amaryar babanki take cawa malamin gaskiya kai baka san aikinka ba. idan ba abun da zaka iyayi ni ina da shi. ha ta mike tana masifa har ta koma gida. [9:59AM, 5/16/2015] Asmeer: Bayan ta koma gida ta ringa sake saken yanda za tayi don ta ga ta kuntatawa mahaifinki sannan ta bakanta miki. ai kuwa tana cikin tunani ne wata dabara ta fado mata sai kawai ta tuntsure da dariya tana cewa tabbas haka zanyi haka zanyi. Bayan kwana biyu ne ta zamto ta je ta samu mahaifinki tana bashi hakurin duk abubuwan da suka faru har da durkusawa a gabansa tana kukan munafunci tana cewa kayafe min mijina na tuba bazan kara ba. sai mahaifinki ya ji tausayin amaryarsa ya ce bakomai amaryata na yafe miki, sai ya kamo kafadunta ya tasar da ita yana cewa ai Allah ma muna masa laifi idan mun nemi gafara a gare shi yana yafe mana. dan haka bakomai na yafe miki. sai ta rungumeshi tana cewa nagode mijina. ke kuwa a lokacin har kin warke sannan kuma a ranar da amaryar babanki take neman gafarar babanki kina cikin daki kina karatu. jin kukan amaryar babanki ne ya sanya kika fito a daki. kina fitowa kuwa amaryar babanki ta je ta rungumeki tana cewa ki ya fe ni "yata na tuba. babanki ne yazo ya kamo hanunki ya zaunar da ke yana cewa ki yafe mata. haka kika ce to dady na yafe mata. "Tabbas da sun san munafuncin da amaryar babanki ta kulla muku da tuni mahaifinki ya saketa ya sallameta, amma da yake rashin sani yafe dare duhu sai babanki ya cigaba da zama da amaryarsa zuciya daya" har ya gaya mata cewa ke ce wannan jaririyar da ta ce yavce ya binneta. sai yavkwashe duk abunbda ya faru ya zayyana mata. sai kawaye ta fashe da kuka tana cewa kaico na...haka dai babanki ya ce bakomai a dai kiyaye gaba. Bayan sati biyu ne da yamma kafin ki dawo a islamiyya ina ganin amaryar babanki ta windon kitchen ta zuba miki abinci a cikin kwanonki wanda aka saba saka miki abinci a cikin. bayan ta zuba ne ta dakko kullin magani a kunkuminta ta barbada miki a ciki. bayan ta gama saka miki ne ta rufe sannan dauki abincin ta kai miki cikin dakinki, cikin murmushi take cewa na tabbata idan tsinanniyar yarinyar nan ta dawo zata bukaci abinci tana zuwa ta ci abincin nan kuwa karshenta yazo. kaga ke nan idan ta mutu mahaifinta zai shiga wani irin hali sannan hankalinsa zai dawo kaina yaso sai na fara juya shi yanda na so. tana gama fadan haka sai ta fice a dakin tana dariyar mugunta. Ni kuwa ganin haka yasa na rikice na rasa mike min dadi, nan da nan sai na ji jikina babu kuzari haka na zauna a kas ina tunanin yanda zan taimake ki daga kisan da amaryar babanki take kokari tayi a kanki. sannan a cikin tunanina nake cewa tabbas inhar na bari aka kashe ki tabbas ban kyauta ba dan haka dole nayi yanda zan taimaka miki. ina cikin wannan halinne wata dabara ta fado min. cikin sauri na je cikin kayana da nake zuwa da su gidanku na dakko maganin mura da yake ina fama da mura dan haka bazan rabu da maganin mura ba. cikin gaggawa na je na dauki abincin da na rage wanda ban cinye ba, sai na daddaka magani guda daya daga cikin magungunan mura na, na zuba a cikin abincin sannan na dauki abincin na je na ajiye a cikin dakinki sannan na dauke wanda amaryar babanki ta kawo miki. "nayi hakanne saboda kubutar da ke daga mutuwa. maganin da nasaka miki kuwa shi zai sanyaki ki barci mai nauyi saboda karfin maganin. idan barci mai nauyi ya dauke ki amaryar babanki za tayi tunanin kin mutu. a ranar kuwa mahaifinki baya gari yayi tafiya zuwa Bauchi. Bayan kin dawo a islamiyya kika bukaci abinci, cikin murmushi da fara"a amaryar babanki ta ce ki je ki dauki abincinki yana cikin dakinki. cikin gaggawa kuwa kika je dakinki kika dauki abincinki kika ci. Bayan minti ashirin da cikin abincinne kika zube kasa barci mai nauyi ya dauke ki tamkar wacce kika mutu. amaryar babanki kuwa lekowa tayi don taga ko kin ci abincin kin mutu. tana ganinki a baje a kas sai ta saka dariyar mugunta bayan ta gama dariyar ta kai tsaye ta kira "yan uwan mijinta aka zo aka duba ki. ganin haka ne suka tabbar kin mutu sai suke cewa mi ya same ki haka kika mutu lokaci guda? sai amaryar babanki tayi karya take cewa bayan kin dawo a islamiyya ne kika ce cikinki na ciwo kafin amaryar babanki ta kawo miki magani har kin mutu. sai kawai ta fashe da kukan munafunki. ko a mahaifinki ba a gayawa a waya ba saboda kar hankalinsa ya tashi. haka aka miki wanka aka sallace ki aka kai ki makabarta aka binne ki.... ....kai! ya ke nan har ansallace ta kuma anbinne ta??? Mu hadu a part 16. don jin yanda zata kasance.TIMA ZAHRA novels / RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 16 RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 16 Posted by Bashir Sani Fesan on 28 Dec 2016 - 13:24 aka sallace ki sannan aka kai makabarta aka binneki. cikin dare na je makabarta ba tare da kowa ya ganni ba na je na tono ki na kai ki gidana. bayan wasu mintuna da tonoki sai kika dawo daga dogon barci da kika yi kina farkawa kuwa. sai kika ganni zaune kusa da ke ina zubar da hawaye. sai kika ce min baaba mai aiki ya na ga kina kuka? kuma ya na ganni a nan ina mamana da dady na? tambayoyin da kika min ne su suka kara sakawa wasu hawayen zubowa daga idanuwana. cikin halin tausayawa tare da goge hawayena na dube ki na ce FATIMA mamanki da babanki sunyi tafiya wani gari shine suka kawo ki gidana ina kulawa da ke kafin su dawo, dan haka a nan gidana zaki zauna har su dawo kin ji?. koda ki ji abun da na gaya miki babu gardamar komai kika ce to shike nan baaba zan zauna. amma kuma har dady na ya dawo daga bauchin? sannan har sun kara wata tafiyar da mama to amma mi yasa basu tafi da ni ba? tambayar da kika min ne na rasa wace irin amsa zan baki, amma a dole na miki karya na ce ai kin san ba a son ayi tafiya da wanda yake barci. da budar bakinki sai kika ce min to ai da sun tashe ni. jin abunda kika fada ne ya kara rikita ni, saboda ina tsoron kar ki gano cewa dady ki da mamanki ba suyi tafiya ba ki ce zaki koma gida. amma cikin wayo da dabara na ce miki ai dady naki baya so idan kina barci a tashe ki saboda yana sonki sosai. sai kika ce to shi ke nan baaba Allah ya dawo da su lafiya. cikin fara"a na ce amin sai tausayinki ya kara kamani a lokacin. sai na rungumeki ina zubar da hawaye. ganin ina zubar da hawaye ne kika ce min baaba to mi yasa kike kuka ne? murmushi kawai na yi tare da goge hawayen dake zubowa daga idanuwa na sannan na ce miki kaina ne yake ciwo bari na je na sha magani . bayan na gaya miki haka ne kafin na fita a dakin sai na mika miki abincin da na tanada miki saboda nasan zaki iya bukatar abinci. kina ganin abincin kuwa kika ce min yunwa kike jima kuwa. sai kawai kika hau cin abincin tamkar wanda ta kwana biyu bata ci komai ba. sai kawai na fita cike da tausayinki. kashe gari da misalin karfe 11 na safe sai ga babanki ya dawo daga bauchi, koda yazo ya taras jama"a a kofar gidansa ana zaman makoki sai ya tsoruta sosai. jikinsa a sanyaye ya shiga da motarsa cikin gida ba tare da yayiwa kowa magana ba. jikinsa na rawa ya shiga cikin gidan da sauri don ya je ya ji abun da ke faruwa. yana shiga kuwa ya taras da matan aure da "yan mata a zazzaune ana karbar gaisuwa har da mahaifiyarsa da sauran "yan uwansa mata da kuma "yan uwan amarya har da ni, ina zaune a gefe nayi jigum. ganin haka ne ya tabbatar mutuwa akayi. koda ya zo zai shiga dakinsa sai ya ji matan da ke zaune suka fara jajanta masa rasuwar da aka yi masa. a cikin jajanta masa ne wasu su ce ya aka ji da rashi kuma? a dole mahaifinki zai amsa da Alhamdulillah. wasu kuma su ce sai dai fa hakuri. jin wasu sun ce ashe Fatima ce lokaci yayi? to Allah ya ba da hakuri. koda ya ji haka ne ya tabbatar ke ce kika rasu. a lokacin kuwa ya fashe da kuka. "tun da nake ban taba ganin mahaifinki yana kuka ba sai wannan ranar. domin kuwa duk abun da ya same shi na kunci wanda ya kai yayi kuka, amma sai dai hawaye su zubo daga idanuwansa. ko a rasuwar mahaifiyarki ma hawaye kawai ya zubar babu sautin kuka." Ganin yanda yake kuka ne matan cikin gidan suka dauki ba shi hakuri. sai kawai amaryar babanki ta tashi ta kama hannunsa ta ja shi cikin dakinsa tana bashi hakuri. ni kuwa ina gefe na sunkuyar da kaina hawaye yana famar su6utowa daga idanuwa na saboda tausayin mahaifinki da ya kamani. sai nake cewa a raina Allah sarki Fatima tana raye amma kuma ana zaman makokinta. Tun ranar da mahaifinki ya ji mutuwarki ya kasance cikin wani irin hali na tausayawa, domin kuwa kullum yana cikin tunaninki ke da mahaifiyarki. duk ya bi ya rame haka mahaifiyarsa za tayi ta masa fada tana cewa ya daina saka damuwa a ransa. duk wanda ya mutu lokacinsa ne yayi muma muna jiran ta mu sai dai muyi fatan kyakykyawan karshe. amma duk da haka bai daina tunaninki ke da mahaifiyarki ba saboda tsantsar son ku da Allah ya jarrabe shi da shi a lokacin tare da danasanin irin abubuwan ta ya aikata muku ke da mahaifiyarki. [9:37AM, 5/17/2015] Asmeer: Ita kuwa amaryar babanki kullum cikin masifa tare da cewa duk kabi ka damu akan wadanda suka mutu alhalin ba dawowa za suyi ba. duk irin wadan nan abubuwan da amaryar babanki take gaya masa bai sa ya daina damuwa da mutuwarku ba. dalilin haka yasa babanki ya daina kula amaryarsa sosai, sannan ya fita daga sha"aninta har ya zamto ya tsaneta a dole yake zama da ita. hakan ya tayarwa amaryar babanki hankali ta rasa mike mata dadi. sannan burin da take a kansa ya gagare ta. haka dai ta kasance cikin kulle kulle da makirci yanda zata shawo kan babanki don tana juya shi yanda yaso. ke kuwa cigaba da zama da ni kika yi. mijina kuwa na sanar masa duk halin da ake ci. da yake mijina mai tausayi ne ya ce bakomai za mu cigaba da zama da ke har lokacin da Allah zai hukunta komawarki wajen iyayenki ba tare da an samu wata matsala ba. haka kuwa muka cigaba da zama dake. sai kuma kusan kullum sai kin min maganar dawowar iyayenki haka zan rarrashe ki na ce zan ce sun kusan dawowa, amma idan basu dawo ba da kaina zan dauke na kai ki garin da suka je. a haka dai har kika ga ji da maganar dawowarsu. Zuwa gidanku dan aikace aikace da na ke yi ban fasa ba kullum ina zuwa. sannan ina ganin duk abun da ke faruwa da iyayenki. sai kuma tausayin mahaifinki ya kama ni bisa halin da yake ciki na damuwa akanki da na mahaifiyarki. ganin haka sai na yanke hukuncin na je na samu mahaifinki a ke6ance na zayyana masa duk makircin da amaryar babanki ta kulla a kanki da kuma gubar da ta saka miki da niyar kashe ki, wanda ake tsammanin kin mutu da kuma ceton da na miki daga sharrin amaryarsa. zan zayyana masa hakane don na ceto shi daga cikin damuwar da yake ciki. Da yamma bayan mahaifinki ya dawo daga office kamar yanda ya saba. sai na nufi dakinsa da nufin zuwa na gaya masa halin da ake ci game da ke. abun mamaki sai na ga dakinsa a bude ba a rufeta ba. domin kuwa duk sanda ya shiga dakinsa ko wani ya shiga dakinsa sai an ja kofar an rufe, amma yau abun mamaki ba a rufeta ba. haka dai na karisa bakin kofar dakin nasa. koda na karisa da nufin sallama da neman izinin shiga abun da na gani ne yayi bala"in tayar min da hankali. domin kuwa amaryar babanki na gani ta cakawa mahaifinki wuka a ciki jini na malala a kasi. cikin calla kara na ruga a guje na fita a gidan, ko takan kayana da nake zuwa gidanku da su ban yi ba na fita a gidan. jikina na rawa na je na fita a gidan har na koma gidana jikina na rawa sannan na gagara magana. ita kuwa amaryar babanki jin ihu na ya sanyata ta fito a dakin a guje ko zare wukar ba tayi a cikin mahaifinki ba. sai ta fito ganina tayi na fita a guje a gida sai kawai ta rikice ta rasa yanda za tayi saboda ta ga lokacin da ta cakawa mahaifinki wuka. babu shiri ta fita a gidan ta je gurin wasu "yan daba ta ce musu maza su bi ni gidana su kashe ni ko nawa suke so zata biya su. "yan daban su biyar ne gingima-gingima majiya karfi sai suka tafo gidana don cika aiki. Ni kuwa bayan na dawo gida na rasa yanda zanyi. sai kawai jikina ya ban cewa amaryar babanki taganni lokacin da ta cakawa mahaifinki wuka dan haka na tabbata nima baza ta bar ni ba gudun kar na tona mata a siri. duk da mijina baya nan haka na dauke ki duk da girman da kike da shi haka na aza ki a bayana na goye ki. na fita a gidan da sauri ko gidan ban rufe ba. sai kawai na doshi hanyar da zata kai ni tashar kano don na gudu na bar cikin garin Azare. ...Allah sarki!!!A ZAHRA novels / RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 17 RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 17 Posted by Bashir Sani Fesan on 28 Dec 2016 - 13:26 sai na nufi hanyar da zata kai ni tashar kano da sauri don na bar garin Azare. jikina na rawa na je na shiga motar Allah ya taimake ni kuwa ina da naira dubu daya da dari biyu a kunkumina ragowar kudin albashina da aka biya ni a gidanku. haka na biya kudin mota har mota ta tashi muka dauki hanyar zuwa kano. sannu sannu bata hana zuwa sai gamu a cikin garin kano. ban tsaya wata wata ba gidan "yan uwan mahaifina nayi kai tsaye jikina na karkawa. Bayan na isa ne da suka ganni cikin wannan hali na tsoruta sai suka ce lafiya kuwa muka ganki cikin wannan dare haka? "da yake sai cikin dare muka isa cikin kano". sai na ce musu gaskiya ba lafiya ba kam. amma su bari idan Allah ya kaimu gobe zan gaya musu komai. haka aka zuba mana abinci ni da ke muka ci har suke tambaya wannan "yar da kika zo da ita fa "yar waye? sai na ce musu su bari zan gaya musu da safe. haka dai aka ba mu masauki muka je muka kwanta ni da ke, nan danan barci ya dauke ki amma ni na gagara barci ina ta tunanin abun da na gani. ina kwance ina tunanin abun da na gani game da abun da amaryar babanki ta aikata ga mahaifinki sai kawai na ji karar wayata ana kirana. jikina na karkarwa na duba mai kirana sai naga lambar Asabe makwabciyata ita take kira. cikin rawar jiki na dauki wayar. jin yanayin muryarta ne ya sanyani na nutsu don na ji mi zata ce min. muryarta tana rawa take ce min kina ina ne? sai na ce mata ina kano yanzu haka. sai ta ce min to wani mummunan al"amari ya faru ga mijinki a cikin gidanki. koda na ji haka sai na ji kirjina ya buga da karfi, sai na ce mata mi ya faru da mijina Asabe? sai take ce min dazu daf da magarib mijinki ya dawo gida amma bai ganki ba shine yake tambaya ta har yanzu baki dawo a wajen aikinki ba ne? sai na ke ce masa kin dawo mana domin kuwa na ji motsin dawowarki. sai yake ce min to ya akai bai ganki ba? sai na ce masa gaskiya ban san ina kika je ba. to shine ya kira lambar wayanki amma sai a ce a rufe take ko babu network. ana cikin haka ne sai wadansu manyan mutane guda biyar suka shiga gidanki suka taras da mijinki. ina jin su suna ce masa a ina kike? sai mijinki ya ce musu yanzu haka yana kokarin nemanki ne, amma su din su waye? cikin daka tsawa suka ce ya fito da ke idan ba haka ba za su kashe shi. jikinsa na rawa ya ce shima bai san inda kika je ba yanzu haka ma nemanki yake a waya. sai suka ce ba za dai ka fito da ita ba ko. sai kawai na ji karar mari tass... sai suka ce muka ce maka ka gaya mana yanda ka 6oye matarka idan ba haka ba za mu kashe ka. shi kuwa mijinki bai san inda kike ba sai ya kara ce musu ban san inda matata ta je ba. ina jinsu suna dukansa sannan suna sara masa adda tun yana ihu har na fara jin yana kalmar shaha har ya daina wato dai sun kashe mijinkin. yanzu haka gawar mijinki na police station ana bincike. koda na ji dukkanin abun da Asabe ta fada sai kawai na ji wani irin hajijiya ya dauke ni ina daga kwance kawai na ba je a kas na suma tamkar wacce ka zarewa rai. can cikin dare na fartado da kaina sai kawai na fashe da kuka ina cewa sun kashe min mijina wayyo! Allah na, haka na ringa kuka a cikin wannan dare ai kuwa sai na ji wani irin matsakaicin ciwon kai ya kama ni. amma ko kadan ciwon kan bai dame ni ba haka na ringa kuka har gari ya waye da kyar na tashi nayi sallar asuba. da safe kuwa "yan gidanmu suka ganni duk fuskata a kunbure. sai suka tambaye ni mike damuna?. sai na kwashe musu dukkanin abubuwan da suka faru da mijina na gaya musu amma kuma ban gaya musu labarinki ba. saboda bana son kowa yasan labarinki gudun kar a ce na miyarki hanun munguwar amaryar babanki. sannan kuma na tabbata mahaifinki ba ya raye bisa caka masa wuka da amaryar babanki ta yi masa. dan haka ba lalle ba ne ace yana raye. to shi yasa na 6oye dukkanin labarinki ban gayawa kowa ba.mijina ne kawai yasan labarinki da abubuwan da suke faruwa a gidanku, shi din ma gashi ya mutu. dan haka babu wanda yasan labarinki sai ni kadai. bayan na gama gaya musu. sun mutukar tausaya min sosai. sai suka ce na kwantar da hankalina a nan gunsu zan zauna har lokacin da komai ya daidaita. haka na kasance cikin tunanin mijina. sannan na kira makwabciya ta na ce mata dan Allah kar ta sake ta gayawa kowa inda nake. sai Asabe makwabciyata ta ce to shi ke nan. ai kuwa da binkice yayi binkice akan mutuwar mijina har kano gidan "yan uwana an zo. amma sai aka ce musu ba a san inda nake ba. haka police din suka koma har dai aka je aka binne mijina sannan aka daina binkicen. Haka muka kasance da ke a nan garin kano ni da ke, kafin na gama takabata ne "yan uwana suke tambayata shin ke din waye ce? amma sai naki na gaya musu gaskiya sai kawai na ce musu ai ke "yata ce jin abun da na ce musu ne suka ce to yaushe akayi aure na har na samu katuwar "ya haka? sai na eh kawai Allah ne ya bani ke. ai kuwa tun daga ranar suke zargina akan cewa cikin shege nayi na haifeki. amma duk da haka ban gaya musu gaskiyar labarinki ba. [8:29AM, 5/18/2015] Asmeer: Muna nan ni da ke a gidan "yanwana bisa zargina da suke yi akaina bisa cikin da nayi na shege har na haifeki. har takai ga cewa suna cewa koma wasu daga cikin "yan iskanane suka je suka kashe mijina. ni dai ban ce musu komai ba. da zama ta kai zama sai suka ce kawai na bar musu gida baza su iya zama da mazinaciya ba. ni kuwa duk da haka ban gaya musu labarinki ba. saboda ina mutukar sonki bana son wani abu ya same ki. haka dai cikin kuka da bakin ciki na dauke ki mu kabar gidan "yan uwana. sai ya zamana na rasa inda za mu je mu. sai kawai na dauke ki muka tafi gidan kakata. kakata kuwa ta ji dadin zuwana sannan ta rike ni ni da ke ba tare da ta tambaye ni labarinki ba. amma tsabar gulma da makirci sai da "yan uwana suka zo gurin kakata suka ce mata kar ta zauna da ni, ni mazinaciya ce. amma kakata ko kulasu bata yi ba. ta ce koma miye haka Allah ya kaddara. haka ta fatattake su, ai kuwa tun daga ranar basu kara zuwa gidan ba. Haka dai muka zauna a gidan kakata, zance aure a gare ni kuwa bana yinsa duk wanda yazo neman aure bana aminnewa da shi. saboda gudun kar a raba ni da ke. haka dai masu neman aurena suka hakura. nima kuwa na zauna a gidan kakata ni da ke to shine har na sakaki a islamiyya a nan garin kano sannan nakanyi sirfe ko sissika da dai sauran sana"o"in da zanyi mu samu kudin da za mu ringa cin abinci ni da ke da kakata sannan kuma na biya miki kudin makaranta. da yake mijin kakata ya jima da rasuwa. to wannan shine labarinki "yata mai cike da tausayi da al"ajabi. shin kina so ki kai ziyara ga amaryar babanki? tambayar da baabata ta min ke nan bayan ta gama gaya min labarina. Duk da yake ni yarinya ce amma da na ji labarina sai da hawaye ya cika idanuwana. cikin damuwa na dago da kaina na ce baabata bazan ta6a zuwa waje "yan uwana ba balantana amaryar babata wacce ta kashe min mahaifi kuma tayi sanadiyar mutuwar mahaifiyata. su kuwa "yan uwana suna ganin halin da nake basu taba zuwa wajena sun taimaka bin ba. to mi zai sa na je wajensu. sai na kara da cewa baabata ina tare da ke har karshen rayuwata bazan ta6a sa6a miki ba sai dai a kuskure. sai kawai baabata ta rungume ni tana kuka tana cewa nima bazan ta6a rabuwa da ke ba ya "yata sai dai mutuwa ta raba mu. sai kawai nima na fashe da kuka aka rasa wanda zai rarrashe mu.... koda hajiya ta ji dukkanin labarin Fatima zahra sai ta fashe da kuka daman tun tana cikin bata labarin hajiya take zubar da hawaye tsabar tausayi da al"jabi da ke cikin laribarin dan haka bayan ta gama jin labarin sai kuka ya kwacewa hajiya sai ta matso kusa da fatima ta rungumeta tana kuka. ita kuwa fatima hawaye ne suka cika idanuwanta sai kawai ta shiga rarrashin hajiya. har hajiya tayi shiru. bayan hajiya ta goge hawayen da suka cika idanuwanta sai ta kara dagowa da kanta ta ce to yanzu ina kakar baabar taki? kuma ya akai baabarki ta daina magana? da fatima ta ji tambayar hajiya sai ta cigaba da bata labarin. ...bayan mun yi sha kuka ni da baabata a lokacin da ta gama bani labarina sai ta janye jikinta daga jikina sannan ta share min hawayena sai ta ce "yata fatima ki daina kuka ina tare da ke ni dai abun da nake so da ke shine ki sirrance wannan labari naki kar ki gayawa kowa har sai na baki izinin fada. sai na ce to baaba insha"allah bazan gayawa kowa ba sai da iziniki.sai ta ce min yauwa "yata Allah ya miki albarka. sai na ce Ameen sai ta ce min to ki tashi ki cire kayanki ki ci abinci sannan ki wanka. sai na ce to baaba haka na tashi na je na cire kayan islamiyayyata na ci abinci sannan nayi wanka kamar yanda baabata ta umarce ni. [9:45AM, 5/18/2015] Asmeer: Zamanmu da baabata da kakar baabata muka cigaba da yi kamar yanda muka saba. bayan wata daya da ban labarina ne da safe bayan mun tashi sai na ga baabata kwance tana kama kanta. sai na tambayeta mike damunta? amma bata ban amsa ba sai kawai tayi nuni da kanta. kakarta ma ta tambayeta abun da ke damunta amma shiru babu magana sai dai tayi mana nuni da hannunta halamar kanta. da muka ga haka cikin sauri kakar baabata ta ce maza na je na kira malam sallau limamin unguwarmu. cikin sauri na tashi ina kuka na je na kira shi. bayan ya zo shi ya dubata sai yayi la"akari da rashin maganar baabata haka dai yayi dube dubensa sannan ya ce gaskiya halamu sun nuna cewa asiri ka yi mata shi ya sanyata rashin magana da ciwon kai. koda na ji haka sai na fashe da kuka. ita kuwa kakar baabata sai ta ce to ya za ayi ke nan? sai malam sallau ya ce eh to akwai maganin da zan rubuta mata tasha. idan anyi da ce ta samu sauki, amma gaskiya asiri aka yi mata babba. sai ya mike ya ce sai a turo wanda zai karbi maganin. sai kakar baabata ta ce na daina kuka na je na karbo maganin da za a bawa baabata tasha ta samu sauki. haka na ta shi na je na karbo maganin. amma koda tasha kanta ne kawai ya daina ciwo. amma babu magana. haka dai muka ringa jika mata magunguna amma duk a banza, gun malamai ma muje amma ba a samu dacewa ba har aka daga gidan da muke ciki aka siyar don nemawa baabata magani amma duk da haka babu labarin samun sauki. haka dai muka hakura muka mikawa Allah komai. tun daga ranar nima na daina zuwa makaranta saboda mai daukar dawainiyata bata da lafiya. abinci kuwa kullum a gidan maigari ake kawo mana. Bayan shekara biyu ne kakar baabata Allah ya mata rasuwa bisa jinyar da tasha fama da ita. ai kuwa bayan wata daya da rasuwar kakar baabata ne masu gidan da muka siyarwa suka bukaci gidansu, haka muka fita a gida muka je gidan "yan uwan baabata amma sai suka yi mana koran kare a dole muka shiga bara ni da baabata don mu samu abun da za mu ci abinci. muhalli kuwa duk gidan da muka sabu a bayan gari wanda aka fara ginawa aka tsaya sai muje mu kwana a ciki idan safiya tayi sai na yiwa baabata jagora mu fita bara don neman abincin da za mu, hatta suturar da za mu saka sai munyi bara tukunna zamu samu wani lokacin ma a kan bola muke tsinar kayan da za mu saka idan na jikin mu suka mutu. Mun shafe shekara uku muna cikin wannan halin ni da baabata sai Allah ya hada mu da yayar manaja wanda yake aiki a babban kamfaninki har ta bamu muhalli sannan take bamu abun da za mu ci, amma da yake mun saba da bara sai mun fita munyi ta. haka dai har Allah ya da mu da ke. wannan shine karshen labarina. Hajiya har a lokacin zubar da hawaye ta ke yi bayan ta gama jin labarin fatima sai ta tausaya mata mutaka sannan ta ce tabbas duk mutum mai imani idan ya ji labarinki dole ya tausaya miku. dan haka na dauki alkawarin kulawa da ke da baabarki har karshen rayuwarku. koda fatima ta ji haka sai hawaye ya kwararo daga idanuwanta sannan ta ce nagode kwarai da gaske hajiya bisa kulawar da kika bamu a baya sannan kika dauki alkawarin cigaba da ba mu kulawa amma kuma kamar yanda na gaya miki a baya kafin na fara baki labari na ce zan miki wasu tambayoyi. cikin murmushi hajiya ta ce haka ne "yata dan haka ina sauraron tambayoyinki ni kuwa insha"allah inhar na san amsoshin tambayoyinki zan baki amsa, harma bana son ace ban san amsoshin su ba. dan haka ina sauraron tambayoyinki. sai fatima ta numfasa sannan ta ce tambayoyin su ne kamar haka: Tambaya ta farko ina ce shin duk wanda ya baki kulawa irin kulawar da baabata ta ban sannan ta kubutar da ke daga kashe kin da aka yi niyya. shin zaki so ta tamkar iyayen da suka haife ki? Tambaya ta biyu shine shin zaki iya rabuwa da ita ki je ki rayu da wasu bayan ita? Tambaya ta uku wacce ita ce ta karshe shin zaki iya fansar da rayuwar wani ko rayuwar wata akan rayuwar ta? ma"ana ki sadaukar da ran wata ko wani wanda ya ke baki kulawa bayan kulawar da ta baki dan ita ta rayu?... .Tab! babbar magana.Ya ke nan????.... Mu hadu a part 18. don jin amsoshin da hajiya zata bawa fatima. Amma idan kai ne ko ke ce wani irin amsoshi zaka/zaki bawa FATIMA ZAHRA?BOOKS [11:08PM, 5/19/2015] Asmeer: <<>>Part 18. Koda hajiya ta ji tambayoyin da Fatima ta mata sai ta sau tattausar murmushi cikin fara"a ta dubi fatima ta ce mata "ya ta fatima ai wadannan tambayoyin naki masu saukin amsawa ne, don haka ki saurari amsoshinsu. amsar tambayarki ta farko ita ce: Tabbas duk mutumin da ya mik irin abubuwan da baabarki ta miki, shin namiji ne ko mace ce babu makawa zaki dauketa tamkar ita ce uwa da uba a gare ki, kai! zaki iya daukanta fiye da iyaye ma. saboda bisa taimakonta ne kika kawo wannan lokacin. kin ga kuwa duk wacce ta miki irin abun da baabarki ta miki ta cancanci ta samu girmamawa da kulawa daga gare ki. Amsar tambayarki ta biyu kuwa ita ce inhar kika gu ji dukkanin wacce ta baki irin kulawar da baabarki ta baki tabbas baki cika "yar halal ba. domin kuwa duk jin dadin da zaki samu kin samu ne bisa taimakon baabarki. dukiya ko mulki ko shugabanki basu kai su rude ki ba har ki gudu ki bar wacce ta baki kulawa kamar yanda baabarki ta baki, inhar ki ka yi haka kuwa babu shakka ba kiyi halacci ba. Amsar ki ta karshe kuwa tabbas zaki iya fansar da ran kowa don ki fanshi ran wacce ta kubutar da naki ran har kika kawo iyanzu, hakkan shine nuna so da kauna a gare ta. ke bari na baki misali kinga duk duniya na fi son dana Asmeer fiye da komai na rayuwa. to ina mai tabbatar miki zan iya fansar da ransa akan ran maccen da ta kula da rayuwata tamkar yanda baabanki ta miki. dan haka ashe kuwa zan iya fansar da ran kowa akan wacce ta bani kulawa. wadannan su ne amsoshin tambayoyinki ya "ya ta. koda Fatima ta ji irin amsoshin da hajiya ta ba ta sai ta fashe ta kuka tamkar baza ta daina ba. da kyar hajiya ta rarrasheta ta yi shiru. sai hajiya ta dubeta ta ce mi yasa ki ke kuka bayan na gama ba ki amsoshin tambayoyinki? shin amsoshin da na baki ba suyi dai dai da amsoshin da kike so ba ne? ko dai nayi kuskure ne a cikin amsoshin da na baki, na gaggauta gyara kuskure na? Da fatima ta ji zantukan hajiya sai ta ce a"a ba haka ba ne hajiya ina kuka ne saboda bana son mutuwa ta raba ni da baabata sannan kuma ina tsoro na yi aure na tafi gidan mijina na bar baabata. wadannan dalililan ne yasa nake kuka. sai hajiya ta ce Allah sarki "ya ta fatima ai mutuwa rigar kowa ce, kowa na jiran ta shi sai dai muyi addu"a Allah yasa muyi kyakykyawar karshe. Aure kuwa shine cikar darajar "ya mace domin kuwa darajarki da kimarki shine gidan mijinki. na tabbata baabarki tana son ta ji ranar da za ki aure saboda darajar da aure yake da shi. to ai idan kin yi aure ba wai kun rabu da baabarki ba ne. kuna tare. dan haka ki daina damuwa kin ji "ya ta. koda fatima ta ji haka cikin sanyin jiki ta ce to hajiya. Allah ya tabbatar mana da mafi alkairi. cikin murna da farin ciki hajiya ta ce Ameen "ya ta haka nake so na ji kin ce. dan haka share hawayenki ki zauna mu ci abinci kinga har dare yayi sosai ga shi kuma har yanzu Asmeer bai dawo ba. sai ta duba a gogon da ke rataye a jikin bango. sai ta ce kinga har karfe 11 da minti 10. jikin fatima a sanyaye ta ce to ki kira Asmeer din mana a waya mu ji lafiya kuwa har yanzu bai dawo ba? murmushi hajiya ta yi sannan ta dakko wayarta tana cewa ina fatan dai kina son dana ko? cikin kunya fatima ta sunkuyar da kanta ba ta ce komai ba. a dai dai lokacinne hajiya ta kai wayarta kunnenta don kiran Asmeer. sai hajiya ta kara sauwa wani murmushin mai dauke da ayar tambaya, sai ta cewa fatima kodai baki son dan nawa ne? kan fatima a sunkuye ta sau "yar gajeriyar dariya tare da rufe fuskarta da hannayenta. sai hajiya ta sau dariya ta ce hmmm....kunyar mi kike ji? kodai kina jin kunyata baza ki iya fada min ba ne? sai fatima ta gyada kai alamar eh. sai hajiya ta kara dubanta ta ce au ni baza a gaya min ba ke nan? to amma kuma ai zaki fadawa dana Asmeer ko? cikin kunya ta ce . sai hajiya ta tutsure da dariya ta ce shi ke nan gobe sai kin gaya masa, kinga na kira wayarsa a rufe, to Allah yasa dai lafiya. sai fatima ta dauke hannunta daga fuskarta ta ce Ameen. sai hajiya ta ce mu ci abincin kawai idan ya dawo ya ci na shi. da kanta hajiya ta zubawa fatima abinci a plate sannan ta zuba a nata. sai suka fara ci har suka kamma. amma Asmeer bai dawo ba. [12:12PM, 5/20/2015] Asmeer: Bayan sun gama cin abincin sai hajiya ta kara dakkowa wayarta ta kira lambar Asmeer amma wayarsa a rufe. sai hajiya ta cewa Fatima kwada kiransa da wayarki ko zata shiga. cikin girmamawa fatima ta dakko ipad din da hajiya ta siya mata ta danna lambar Asmeer amma bata shiga ba. sai ta gayawa hajiya lambar fa bata shiga ba. sai hajiya ta ce Allah yasa dai lafiya. sai fatima ta ce Ameen. Da yake dare yayi sosai sai hajiya ta umarci fatima da ta je ta kwanta ita za ta jira Asmeer a nan har ya dawo. sai fatima ta ce a"a mu zauna dai har ya dawo. haka dai suka cigaba da zama suna hira. har barci ya fara daukar hajiya ta fara gyangyadi, a dole hajiya ta tashi ta tafi dakinta ta kwanta. ita ma fatima tashi tayi ta tafi dakinta. Fatima gagara barci tayi a wannan daren tana ta tunanin baabarta tare da aikin da aka saka ta na sakawa hajiya da dan ta Asmeer guba a abinci. ga shi kuma lokacin da ya kamata ta aikata aikin da aka saka ta ya wuce. sai kawai ta fashe da kuka ta na fadin wayyo! Allah na za su kashe min baabata. sai ta ji kamar a lokacin ta tashi ta je ta nemo Asmeer a duk inda yake ta kawo shi gida ta saka musu guba a abinci su ci don ta ku6utar da baabarta daga kisan da azzaluman mutanen da za su aikata a kanta. tana cikin kukan ne ta yi tunanin cewa kukan da take yi ba zai taimake ta da komai ba. abun da ya kamata tayi shine ta tashi tayi alwala tayi nafiloli ta roki Allah ya kare mata baabarta daga sharrin azzaluman mutanen da suka kamata. sannan Allah ya tona asirin su baya ga haka kar Allah ya ba ta ikon sakawa hajiya da danta Asmeer saka musu guba a cikin abinci. mikewa tayi ta je tayi alwala ta shinfida garduma (sallaya) sannan tayi salloli nafila. bayan ta idar tayi addu"o"i ta shafa. sannan tana kuka ta koma ta kwanta. kwanciyarta ke da wuya ta ji an kira sallar asuba. haka ta kara mikewa ta tashi tayi sallar asuba. bata koma barci ba sai ta dakko alkur"ani mai girma ta karanta yanda ya sauwaka har gari ya waye. Tun kafin gari ya gama waye hajiya hajiya ta zo ta kwankwasa dakin fatima. fatima kuwa na zaune a kan garduma ta tashi ta je ta bude kofar dakin. koda ta ga hajiya sai ta durkusa a gabanta sannan ta gaishe da hajiya. cikin murmushi hajiya ta amsa gaisuwar sannan ta cewa fatima Asmeer fa bai kwana a gida ba. da fatima ta ji haka jikinta a sanyaye ta ce to ina Asmeer ya je haka? bai kwana a gida ba? Allah yasa dai lafiya. hajiya dogon numfashi ta ja ta ce Ameen. yanzu ki zo mu je muyi breakfast gashi can na hada mana da kaina dan haka muje mu karya kumallo. cikin sanyin jiki fatima ta cire hijabinta ajiye akan garduma sannan ta ja kofar dakinta ta rufe. sai ta biyo bayan hajiya suka je suka zauna akan kujerun da ke wajen cin abincin. bayan sun zauna sai hajiya ta bude plate din da ke dauke da soyayyun doya da kwai, sai ta dakko emty plate dake kan table ta zuba sannan ta bude kular dake ajiye a gefe dake kan table sai ga farfesun naman kaji a ciki haka da diba ta zuba a geban suyayyun doyan da ta zuba a plate. bayan ta gama zubawa sai ta ajiye a gaban fatima. sai hajiya ta kara yunkura zata dauki plask din ruwan tea sai fatima tayi saurin dauki plask din tana fadin haba! hajiya ai dawainiyar zai yi yawa. sai hajiya ta yi murmushi ta ce to dan nayi dawainiya ga kyata kuma sirukata ai ba abun damuwa ba ne. sai fatima ta sau guntun murmushi sai ta ce haka ne sannan ta dauki emty plate ta zuba soyayyon doya da kwai da farfesun naman kaji kamar da yanda hajiya tayi. bayan ta gama zubawa sai ta hada tea mai kauri a cikin kofina biyu sai ta ajiye daya a gaban hajiya dayan kuma ta ajiye a gabanta. Bayan ta kammata sai hajiya ta ce kai sirukan nan tawa tana sona. sai fatima tayi murmushi sannan hajiya ta dauki chokali da nufin cin abinci sai ta ji wayarta tana ringin a dakinta. amma sai tayi kamar bata ji ba. sai ta debon abincin zata ci sai ta ji an kara kiranta a dole ta tashi ta je ta dakko wayar. bayan ta gama amsa wayar ne sai ta dauki chokalin da yake cikin abincinta ta fara ci. ita kuwa fatima koda ta kai abincin a bakinta sai ta ji zuciyarta ta tashi sai kawai tayi tari cikin sauri ta ajiye abincin ta cigaba da tari. koda hajiya ta ji tarin fatima yayi yawa sai ta ce maza tashi ki je ki dakko ruwa a firij ki sha. cikin girmamawa fatima ta tashi ta je dakkowa ruwa. sai da fatima ta dauki wasu mintuna sannan ta dawo. koda ta dawo wajen da suke cin abinci da hajiya, sai fatima ta zo ta taras hajiya kwance kumfa na zuba daga bakinta da hancinta. a firgice fatima ta kwalla ihu. ai kuwa sai ga masu aikin gidan sun fito da sauri. koda suka ga halin da hajiya take ciki sai suka gaggauta kiran direban gidan aka dauki hajiya aka nufi asibiti da ita cikin gaggawa.... ....Ya ke nan mi ya samu hajiya haka?...ku biyo ni a part 19 don jin abun da ya faru ga hajiya. Naku ASMEER. ina mai baku hakurin rasMA ZAHRA novels / RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 19 RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 19 Posted by Bashir Sani Fesan on 28 Dec 2016 - 13:30 aka dauki hajiya aka nufi asibiti da ita cikin gaggawa. *** *** *** Ita kuwa fatima ganin an dauki hajiya an nufi asibiti da ita, cikin sauri ita ma ta fita ta nufi can kauyensu gidan da aka tsare baabarta. jikinta na rawa tare da waige- waige har ta isa bakin gidan da aka tsare baabarta. kirjinta na bugawa da karfi ta shiga cikin gidan koda ta shiga aciki sai ta ga babu kowa a ciki sai ta fara leke-leken dakunan gidan tana cewa kuna ina ku fito min da baabata. tana cikin fadan haka sai ta ji muryar ainihin ogan mutanen wanda shi ya sakata aikin. cikin sauri ta juya baya sai ta ga mutumin fuskarsa cike da murmushi sai kawai ya tuntsire da dariya kamar ba zai daina ba. ita kuwa fatima cewa take yi ina baabata ku fito min da ita mana sai dariya kake min. shi kuwa dariyarsa ya cigaba da yi sai kawai yayi tafi, lokaci guda yaransa suka fiffito suka kewaye wajen. Fatima kamewa tayi tare da yin mamaki bisa abun da ta ga ni. abun da ta gani kuwa Larai mai aiki a gidan hajiya ta ga ne tare da wadanan mutane ita ma tana dariya. sai kawai fatima ta bude baki cikin mamaki ta ce ke kuma larai mi ya kawo ki nan alhalin a gidan hajiya kike aiki sannan kuma har da ke aka tafi kaiwa hajiya asibiti??? babu wanda ya bawa fatima amsar tambayarta sai kawai ogan azzaluman mutanen yayi nuni da daya daga cikin yaransa da su miko masa abun da yake hannunsa. cikin cika umarni ya miko masa. shi kuma ogan sai ya chillawa fatima abun da aka mikawa ogan. Cikin sanyin jiki tare da rawar jiki fatima ta durkusa ta dakko abun da ogan ya cillo mata. ba wani abu ba ne dankwalin baabar fatima ne duk jini ya 6ata shi. wasu zafafan hawaye ne suka kwararo daga idanuwanta sai ta dago da kanta ta kalli ogan ta ce ina baabar tawa? dariya ya kara tuntsurewa da shi sannan ya dubeta ya ce baabarki ta mutu domin kuwa jiya da daddare muna tattaunawa irin kisan da za mu mata sai kawai muka ji an dirka ta baya sai muka je muka leka sai muka hango baabarki tana gudu sai nasa yarana suka bita a bayan don su kamota su dawo da ita. can bayan sun dawo sai suka dawo rike da wannan dan kwalin baaabarki duk jini ya bata shi. sai suke ce ai bayan sun bi baabarki sai da ta shiga har cikin gari sun kusan kamata ke nan sai ta tsallaka titi wani mai mota ya bigeta yanayin yanda ya bigeta ne suka tabbatar abu mawuyaci ne ta rayu, amma haka mai motan ya fito ya dauketa duk jini a hancinta da bakinta da kuma sauran sassan jikinta na zuba. ya dauke ta ya sakata a mota ya tafi da ita. su kuma yarana sai suka je dai dai yanda motar ta buge baabarki suka ga wannan dan kwalin suka dakko shi suka kawo min don ya zama sheda a gare ni sannan kema ya zama sheda a gare ki. To ganin abun da ya faru ne na ce tabbas inhar kika ji mutuwar baabarki a wannan daren babu shakka zaki iya fasa aikata abun da muka sakaki sannan zaki tona asirin abun da muka sakaki. shi yasa na kira mai gidana wanda ya saka mu wannan aikin shine ya ce yasan abun za ayi. to a cikin wannan daren ya je gidan hajiya a sirrance ya je ya samu wannan macen wacce na ji kin kira sunanta barai ko Larai? bayan ya sameta sai ya ce mata yana son ta yi masa wani aiki ne. shine ta bukaci ta ji wani aiki ne? shine ya mika mata irin gubar da muka ba ki a leda. bayan ya mika mata ta kar6a. sai ta ce miye wannan kuma? shine yake ce mata guba ne a ciki ina son ki zuba a cikin abincin hajiya da na Asmeer tare da na fatimq duk su ci su mutu. to da ta ji haka ne sai ta tsoruta ta ce baza ta iya ba. a take a wajen ya zaro dumin kudi "yan dubu dubu ya mika mata ya ce ki karbi wannan naki ne na baki kyauta, sannan idan kin aikata abun da na sakaki zan baki ninki goma na wannan kudin da na baki yanzu baya ga haka zan baki dukkanin abun da kike so na more rayuwa sannan zan kaiki saudiya da sauran kashen kasar wajen. ni dai ki aikata abun da na sakaki. koda Larai ta ga wannan dumin kudin a hannunta sannan ta ji dukkanin abun da maigidana ya gaya mata cikin rawar jiki ta ce ta amince zata aikata dukkanin abun da ya sakata. haka suka yi sallama ya tafi ita kuma ta kuma cikin gidan hajiya ba tare da kowa ya gan su ba. da sassafe kuwa Larai ta tashi ta je za ta hadawa hajiya kayan breakfast kamar yanda ta saba. amma sai hajiya ta ce a"a ta bari kar tayi. yau ita zata hada kayan breakfast. kamar yanda Larai ta zo ta yi mana dukkanin bayanin yanda ta sakawa hajiya guba da kuma ke sai ta ce to bayan hajiya ta gama hada muku kayan breakfasta sai ta tafi don ta kira ki a dakinki. to a dai dai wannan lokacin ne Larai ta je ta saka muku guba a cikin kayan breakfast din da hajiya ta hada muku. [8:59AM, 5/22/2015] Asmeer: Sai dai kuma kash! Allah ya ku6utar da ke da Asmeer baku ci abincin ba hajiya ce kawai ta ci. to bayan kinyi ihu an zo an dauki hajiya zuwa asibiti sai Larai ta sulale ta hau taxi ta taho nan ta sanar mana duk abun da ya faru. dan haka kar ki mamaki ganin Larai a nan domin kuwa kudi ne ya kawo ta nan. Bayan ogan azzaluman mutanen wanda ake kiransa da bakin arne ya zo dai dai nan a bayaninsa sai ya numfasa ya kara kallon fatima ya ce baki aikata komai game da abun da muka sakaki ba, dan haka akwai wani aiki da za mu kara sakaki, inhar baki aikata abun da muka sakaki ba a wannan karon babu shakka kashe ki za mu yi. kuma ki sani a cikin ma"aikatan gidan hajiya muna da mai leken asiri wanda yake gano mana duk abun da ke faruwa a gidan hajiya. ta dalilinsa ne muke sanin duk wani motsinki da na hajiya da danta Asmeer. dan haka inhar kika sake kika yi kokarin tona mana asiri ko ki ka ki aikata abun da muka saka ki za mu sani a gun mai leken asirin gidan hajiya inhar kuwa muka san zaki tona mana asiri to kashe ki za muyi. sai bakin arne ya gyara zama sannan ya fuskanci fatima ya ce yanzu abun da muke so ki kara aikatawa shine: ina son yau din nan ki zo mana da Asmeer nan gida bisa yaudara da jan hankalinsa da za kiyi, inhar kin aikata haka babu shakka ke kin tsira daga kashe ki da muka yi niyar yi sannan kuma za mu baki.... kafin ya karisa maganar sai kawai suka ga fatima ta sulale kasa. koda suka dubata sai suka ga ta suma. sai ogan wato bakin arne ya tuntsure da dariya ya cewa Larai maza debo mana ruwa ki watsawa wannan matsiyaciyar ta tashi ta je ta aikata abun da muka sakata. cikin gaggawa larai da je ta debo ruwa ta watsa mata. cikin gigita fatima ta dawo daga suman da tayi sai kawai ta fashe da kuka tana cewa sun kashe min baabata wayyo! Allah na shiga uku. shi kuwa ogan azzaluman dakawa fatima tsawa yayi sannan ya ce maza ki tashi ki fita ki je ki tafo mana da Asmeer nan. ita kuwa fatim kuka ta cigaba da yi ko kula bakin arne ba tayi ba. shi kuwa da ya ga haka sai yasa larai da daya daga cikin yaransa da su dauketa su je su sakata a motarsu da take fake a bayan gidan nan su je su ajiyeta a can gefen gari su dawo. cikin cika umarni Larai ta cincibi fatima ta je da sakata a mota sannan daya daga cikin yaran bakin arne wanda shine direba ya ja mota ya nufi can cikin gari. **** *** *** A can asibiti kuwa bayan an kai hajiya sai aka yi waya a Asmeer aka yi sa"a kuwa wayarsa ta shiga sai aka sanar masa halin da hajiya take ciki. cikin gaggawa ya baro wajen da yake ya zo asibitin da aka kawo hajiya. bayan ya zo shi sai ya taras masu aikin gidansu a tsugunne sunyi tagumi. jikin Asmeer na rawa ya tambaye su ina hajiyan? jummai ce ta ce masa tana ciki likita yana dubata shine ya ce mu tsaya a nan. sai Asmeer ya yunkura zai shiga ciki sai wani wanda yake kula da wajen ya cewa Asmeer dakata malam baka ji abun da suka gaya maka ba ne? sai Asmeer ya ce uwata ce fa ya ba zan je na ga halin da take ciki ba? sai mai tsaron wajen ya ce to kayi hakuri mana ai ba a shiga wajen har sai likita ya fito ya bada umarnin shiga. A dole dai Asmeer ya hakura ya fara safa da marwa a wajen yana rike hannu yana cewa Allah ya baki lafiya hajiya. sai kawai ya waiga wajen jummai ya ce mi ya samu hajiyan ne haka? sai jummai ta gaya masa abun da ya faru na ihun da fatima tayi da zuwa daukan hajiya da suka yi kumfa na zuba daga bakinta har sua kawo nan asibitin. tana gama sanar da shi sai likita ya fito a dakin da hajiya ta ke. ai kuwa sai Asmeer da masu aikin gidan hajiya suka yi caaa a kansa suna cewa ya jikin hajiya? Sai likitan ya ce eh bisa binciken da nayi na gano cewa hajiya dai guba ta ci a cikin abinci amma Alhamdulillah! jikinta da sauki. amma da baku gaggauta kawo ta ba inhar gubar tafi karfin jikinta da tuni ta rasa ranta. dan haka zaku iya shiga ciki, sannan waye Asmeer da Fatima a cikinku? tambayar da likita ya musu ke nan. sai Asmeer ya ce nine Asmeer sai ya duba cikin masu aikin gidansu bai ga fatima ba. sai ya ce musu ina fatiman kuma? sai masu aikin gidan hajiyan su kace masa mun baro ta a gida, amma musan zata zo ta. Da Asmeer ya ji haka sai ya cewa likita fatima tana gida amma zata zota. sai likitan yace eh daman ba wani abu ba ne illa jin sunanka da sunan fatima da nake ji a bakin hajiya. amma zaku iya shiga ciki sai dai kar ku tashi hajiya daga barcin da take yi saboda na mata allurar bacci don ta samu hutu. dan haka kar ku tasheta har sai ta tashi da kanta. cewa suka yi to! doctor sai suka shiga cikin dakin cike da murna.hin ganin posting din da wuri bisa jarrabawar da za mu fara yau.MA ZAHRA novels / RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 20 RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 20 Posted by Bashir Sani Fesan on 28 Dec 2016 - 13:32 sai suka shiga cikin dakin suna murna. *** *** *** Fatima kuwa lokacin da direban bakin arne tare da Larai suka a jiyeta a gefen titi bayan sun kawo ta bayan garin sai suka juya suka barta a nan tana kuka. gagara tashi tayi tana ta shekan kukanta sai da zafin rana ya bigeta tukun ta tashi tamkar wacce ta zauce. haka ta doshi cikin gari ba tare da ta san ina ta nufa ba. har a lokacin kuwa tana rike da dan kwalin baabarta dan haka duk lokacin da dago ta ga wannan dan kwalin sai ta kara fashewa da kuka. har ya zamana ta gigita sosai sannan kanta ya fara ciwo ga kuma yunwa ta fara galabaitar da ita. tana cikin tafiya tana tangadi ta nufi gidan hajiya. Isarta bakin get din gidan hajiya ne ta tuno ashe fa hajiya an dauketa an kaita asibiti. dan haka cikin gaggawa ta shige gidan tana shiga ciki kuwa jiri ya debeta ta fadi koda mai gadi ya ga haka sai yazo ya tsaya a gaban fatima yana fadin subhanallah! mi ya same ki ranki dade? amma ita kuwa sai famar nishi take yi tana daga kwance sannan tana kiran ruwa! ruwa!!ruwa!!! tare da fadin kaina! kaina!! kaina!!!. a dai dai lokacin ne sai ga jummai jikinta na karkarwa ta dawo daga asibiti ta shiga cikin gidan, ai kuwa mai gadi yana ganin jummai ya ce yauwa maza hanzarta ki zo ki taimaka mata ki shiga da ita ciki. haka jummai ta cincibi fatima ta shiga da ita ciki ta kwantar da ita akan kujera a falo sannan ta je ta debo ruwa ta kawo mata. shan ruwan fatima ke da wuya sai ta ji wani irin kasala ya shige ta sai kawai ta linshe idanuwanta kamar mai barci. Jummai kuwa koda ta ga fatima ta linshe idanuwanta tayi tsammanin fatima barci tayi don haka jikinta na rawa ta tashi ta je ta shiga dakinsu na masu aiki. "Ashe wayarta ta manta a dakin kuma tana so ta yi waya dalilinta na dawo daga asibiti wajen hajiya." bayan ta dauki wayan sai ta buga waya. Ashe fatima tana jin duk wayar da jummai ta ke yi don haka sai ta ji wani irin tsoro ya kamata tare da mamaki game da jin wayar da jummai take yi. haka fatima ta kafa kunnenta ta ji dukkanin wayar da jummai take yi. tayi niyyar ta tashi ta nufi asibitin da aka kwantar da hajiya, amma sai tayi tunanin inhar ta tashi ta fita to jummai zata zargeta akan jin wayar da jummai ta yi ne yayi sanadiyar gudunta dan haka gwanda ta kwanata har jummai din ta zota sannan ta roketa ta kaita asibitin da aka kwantar da hajiya don ta duba lafiyarta. tabban dalilin da yasa fatima taki guduwa shine tabbas ta fara ganowa duk wasu makirci da munafurcin da ake kullawa ya fara bayyana dan haka ya sanyata ta tsaya don tasan matakin da zata dauka don kare hajiya daga sharrin da yake shirin faruwa a gareta. saboda yanzu hajiya ce gatar fatima. Bayan jummai ta kammala wayarta sai ta fito ta zauna kusa ta fatima wacce take kwance a kan kujera. fatima kuwa ta ji lokacin da jummai ta zo ta dan haka sai ta danyi juyi kamar mai barci koda tayi juyi sai ta mike ta zauna tana hamma. duk da fatima ta san halin da hajiya take ci amma sai ta tambayi jummai cewa ina hajiya take? sai jummai ta ce au ke baki san an kaita asibiti ba? sai fatima ta mata karyar cewa ai tun lokacin da naga kun fita da hajiya kuka nufi asibiti da ita ban san ina kaina yake ba. sai jummai ta ce Ayyah! ai tun lokacin da muka kai hajiya asibiti bayan likita ya dubata sai yake ce mana guba aka zuba mata a abincin, amma jikin nata da sauki amma na barota a can asibiti tana barci. na dawo ne don na dafa mata ruwan zafi na kaimata ko zata bukaci ruwan zafin. "karyar da jummai tayi ke nan. alhalin ba haka ba ne" Da fatima ta ji jummai ta ce jikin hajiyan da sauki sai tayi mutukar farin ciki sai ta cewa jummai to ki hanzarta ki je ki dafa mata zuwan zafinki zo mu tafi. haka jummai ta mike ta je ta dafa ruwan zafi ta saka a plask ta zo suka tafi asibitin da aka kwantar da hajiya. *** *** *** Asmeer a durkushe yake akan gwiwoyinsa a gaban gadon da hajiye take kwance idanunsa sun cika da kwanlla ya zurawa hajiya idanu yana kallonta. su kuwa masu aikin gidan hajiya a tsaye suke a gefe sunyi jigum suna ta kallon hajiya. ita kuwa hajiya a kwance take tana ta barci. can zuwa wani lokaci sai hajiya tayi motsi sannan ta bude idanuwanta a hankali. Ganin hajiya ta tashi Asmeer ya sau wata murmushi mai dauke da murna da farin ciki, sai ya fara cewa sannu hajiya! sannu hajiya!!. ita kuwa hajiya waigawa wajen masu aikin ta tayi ta bi su da kallo. su kuwa masu aikin sai cewa suke sannu hajiya ya jiki? bayan hajiya ta gama kallonsu gaba ki daya sai ta yunkura ta tashi ta zauna sannan ta ce ina FATIMA? abun da ya basu mamaki ke nan. shima Asmeer yayi mamakin hajiya da ta fara buden bakinta ta tambayi Fatima. sai kawai Asmeer ya ce mata eh tana gida amma zata zo ta. sai hajiya ta ce to amma ya na ganni a nan waya kawo ni asibiti kuma? sai Asmeer ya ce za a gaya miki amma ki bari ki huta tukunnan. Hajiya kallon Asmeer tayi cikin mamaki sannan ta budi baki ta ce ina ka je jiya baka kwana a gida ba sannan na kira wayanka a rufe? sai Asmeer ya numfasa kadan sannan ya ce ki hakuri hajiya. jiya bayan na kai sakon da abokina ya ban na kai gidansu a kan hanyata ta dawowa ne na bige wata mata a kan titi. shine na dauke ta nayi saurin kaita asibiti bisa jinin da yake zuba a jikinta. bayan na je asibitin ne sai suka ce baza su karbeta ba sai da police haka cikin dare na je police station na je ta tafo police. haka aka karbeta aka dubata. amma da yake ni na kawo ta babu damar tafiya har sai na ga an gama duba matar. bayan an gama dubata sai aka ce dole a bata gado. haka na zauna tare da ita. wayata kuma a lokacin babu charge na so na kira kki na sanar miki halin da ake ciki amma Allah bai bani ikon karbar wayar wani na kira ki ba. to sai dazunnan da safe bayan na ciro wayataa motor daga charge na danna zan kira ki ke nan sai naga kira bayan na dauka ake ce min ai baki da lafiya kina asibiti. haka na gaggauta zuwa don naga halin da kike ciki. [10:50AM, 5/24/2015] Asmeer: Bayan hajiya ta gama jin dukkanin bayanan Asmeer sai ta ce Ayyah! ai ban san abun da ya faru da kai ba ke nan, amma ya jikin matar? sai Asmeer ya ce da sauki. sai hajiya ta kara cewa amma waye a wajenta? sai Asmeer ya ce babu kowa a gunta. sai hajiya ta ce to ya kamata ka koma ko zata bukaci wani abun. sai Asmeer ya ce haba! hajiya ke da baki da lafiya zan koma wajenta. sai hajiya ta ce eh ai dole ka koma saboda matar bata da kowa sai kai wanda ka kaita. suna cikin haka ne sai Jummai da fatima suka turo kofa tare da yin sallama. bayan an amsa musu sallama sai suka shigo suka durkusa a gaban hajiya suka ce ya jiki? cikin fara"a hajiya ta amsa da sauki. bayan sun tashi sun koma gefe sun tsaya. sai hajiya ta kalli fatima ta ce tun da zo ina tambayarki sai aka ce min kina gida. ina fatan lafiya ko? kan fatima a sunkuye ta ce eh lafiya kalau hajiya. sai hajiya ta ce to madallah tunda lafiya. can zuwa wasu lokuta sai hajiya ta cewa Asmeer to sai ka tashi ka je gun matar ka dubata a asibitin. cikin ladabi ya ce to shi ke nan hajiya. sai ya mike da nufin fita. sai fatima ta ce waye ba lafiya kuma za ka je gunta a asibiti? cikin fara"a Asmeer ya waigo ya cewa fatima zan je na duba matar da na bige jiya da daddare ne. sai fatima ta ji kirjinta ya dan buga, sai ta ce wace mata ce? sai ya ce nima ba santa ba jiya dai da daddare na bigeta. sai jikinta yayi sanyi bata kara cewa Asmeer komai ba har ya fita. Haka Fatima da hajiya suka zauna suna ta hira. su kuwa masu aikin gidan hajiya, hajiya ce ta ce musu su tafi gidanta su cigaba da aikinsu domin kuwa ta ji likita ya ce da yamma zai sallameta haka suka fita suka tafi gidan hajiya. Fatima kuwa kasancewa suka yi da hajiya a nan asibitin salla ce kawai take barin hirar da suke yi su je suyi har yamma tayi. Misalin karfe 4:00pm na yamma sai ga doctor ya shigo cikin dakin duk jikinsa a sanyaye sai ya zo ya taras da hajiya zaune. ita kuwa fatima a lokacin da shiga toilet don ta kama ruwa. koda hajiya ta ga doctor cikin murmushi ta ce sannu da zuwa. jikinsa a sanyaye ya ce yauwa hajiya. cikin murna hajiya ta ce ai tun dazu nake jiranka kazo ka sallame ni. domin kuwa har na gama shirye shiryena na tafiya. cikin wani irin hali doctor ya ce hajiya tabbas yanzu na so na sallame ki amma kuma hakan baza ta yiwu ba. cikin mamaki hajiya ta ce saboda mi? sai doctor ya kalleta a lokacin da hawaye ya cika idanuwansa sannan ya ce hajiya tabbas ni ban kasance likita mai zalintar marasa lafiya ba sannan ba kasance wanda za a hada baki da ni a kashe wani ko a zalinci wani ba saboda abun duniya. jikin hajiya sanyi yayi sannan ta kalleshi cikin mamaki ta ce ban fahimci mi kake nufi ba likita. sai doctor ya ce hajiya abun da nake so na ce miki shine an bani makudan kudi don nazo na miki allurar mutu. hajiya tana jin haka sai ta dafa kirjinta sannan ta ja dogon numfashi sannan ta ce allurar mutuwa fa ka ce doctor. sai doctor ya ce eh! allurar mutuwa aka ce na miki don ki mutu. domin kuwa dazu da misalin karfe 2:00pm bayan na je gidana sai wasu mutane wanda ban san ko suwaye ba tare da makamai adadinsu sunkai goma. suka zo suka ce min suna so na musu wani aiki. sai na ce musu to su bari na koma asibiti yaso sai sukai maras lafiya na duba shi sai na masa aikin. sai suka ce ba irin wannan aikin ba suna so na zo na miki allura mutuwa idan an miki kin mutu sai na ce gubar da aka saka miki a abinci ne yayi sanadiyar mutuwarki. sai na ce gaskiya bazan iya ba. sai suka fiddo ta dumin kudi suka ce ga wannan idan na gama aiki zasu ban naira millon goma da mota da gida sannan sai na bukacin duk abun da nake so. sai nanuna masu sam bazan iya kashe wani akan abun duniya ba. da suka ga bazan aikata abun da suka sakani ba sai suka kama matata da "ya "yana biyu suka ce inhar ban aikata abun da suka saka ni ba za su kashe iyalina sannan nima su kashe ni. ni kuwa ina son "ya "yana da mata ta. sai na ce to suyi hakuri zan aikata abun da suke so. to shine suka tafi da iyalina su ka ce idan na aikata abun da suka sakani za su saki iyalina amma idan ban aika ba tabbas za su zo su jefar da gawarwakin mata ta da "ya "yana a kofar gida. na ji tsoro kwarai da gaske shi yasa na zo wajenki don na aikata abun da suka umarce ni don na ceto iyalina daga mutuwa sannan nima na tsira daga kashe ni da suka ce za suyi... ...too fa! ana wata ga wata???Home / RAYUWAR FATIMA ZAHRA novels / RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 21 RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 21 Posted by Bashir Sani Fesan on 28 Dec 2016 - 13:34 ....Sannan nima na tsira daga kashe ni da suka ce za suyi. gama fadin haka ke da wuya sai likita ya fiddo ta allura sannan yayi kan hajiya gadan gadan idanuwansa sun cika da kwalla. ita kuwa hajiya tana daga kwance a kan gado koda ta ga doctor ya iyo kanta sai ta fara cewa likita mi kake shirin aikatawa a kaina sai ta yunkura zata tashi. koda likita yazo daf da ita babu zato babu zammani sai doctor yaga fatima ta tsaya a gaban hajiya tana cewa dakata doctor na ji duk maganar da ka fadawa hajiya dan haka akwai maganar da zan gaya maka wacce zata taimake mu gaba ki daya ba tare da ka aikata abun da kake shirin aikatawa ba. tsayawa likita yayi sannan ya kalli fatima ya ce ke kuma wace ce da zaki zo ki tsaya a gaban hajiya? sai fatima ta ce ni sunana fatima, kuma ina dauke da muhimmiyar magana da zan fada yanzu wacce zata taimaki hajiya waje bayyanar mata munafunci da ake shiryawa hajiya ita da dan ta Asmeer da kuma shirin da aike shiyawa don a kashe hajiya da danta Asmeer. Haka zalika kaima doctor abun da zan gaya yanzu shi zai bada dama wajen kubutar da iyalinka, amma bazan fadi komai ba sai Asmeer yana nan. kasancewarsa a nan yana da muhimmanci sosai. Hajiya tana daga kwance sai ta mike ta zauna bisa jin abun da Fatima ta fada. shi kuwa doctor cika yayi da mamaki game da abun da fatima ta ce. sai ya ce ya kamata ki sanar mana ko miye ba sai Asmeer yana nan ba tunda hajiya tana nan. hajiya kuwa cewa tayi "yata ki gaggauta sanar mana abun da yanke kunshe wanda ake kokarin ganin bayana ni da dana. sai fatima ta numfasa ta ce hajiya ke dai a kira Asmeer din domin kuwa maganar da zan fada tafi kusa da shi. koda hajiya ta ji haka sai ta dauki waya wacce take kusa da ita ta kira lambar Asmeer. bayan Asmeer ya dauki wayar sai hajiya ta ce maza ka gaggauta zuwa. cikin ladabi ya ce to hajiya gani nan ina zuwa. bai dauki lokaci mai tsawo ba sai ga Asmeer ya shigo cikin dakin da a kwantar da hajiya, ganin yanda hajiya da fatima da kuma Doctor suka yi jugum ne ya sanya jikinsa yayi sanyi. bayan ya kariso wajen sai ya kalli hajiya cikin sassanyar murya ya ce gani hajiya. sai hajiya ta kalli fatima ta ce to ga Asmeer din ya zo sai ki fa di abun da ki ce zaki fada. cikin murmushi fatima ta kalli Asmeer daga bisani kuma sai hawaye ya kwararo daga idanuwanta. abun da ya bawa su hajiya mamaki ke nan sai Asmeer ya ce my sister miye dalilin zubar da hawayenki? sannan kuma mi zaki fada da kika nemi na zo? sai fatima ta ce brother na tabbas ina zubar da hawayen ne bisa maganar da zan gaya muku yanzu. jikin Asmeer sanyi yayi sai nan ya dubeta ya ce wace irin magana ce haka? sai fatima ta kalli hajiya sannan ta kalli Asmeer sannan ta fara cewa. yau wajen kwana hudu ke nan da kama baabata wacce aka tsareta a can kauyen da muke zaune a wani sabon gida da ake ginawa. sai fatima ta kwashe duk abun da ya faru tun daga ranar da driver ya kaita gida da takardar da aka bawa yayar manaja don ta bawa fatima har zuwa lokacin da aka zuba musu guba a abinci don su ci su mutu. da kuma komawar fatima wajen azzaluman mutanen nan da suka umarceta ta tafo da Asmeer zuwa wannan gidan da kuma dakkota da akayi aka jefar da ita har ta je gidan hajiya. koda ta zo wajen da ta ji jummai tana waya sai wasu hawaye suka kara kwararowa daga idanwanta sannan ta cigaba da gaya musu tana cewa abun da na ji jummai tana cewa shine oga hajiya fa ba bata mutu ba ya kamata a san abun da za ayi. domin kuwa yanzu na dawo daga asibitin, likita ne ya ce gubar da hajiyan ta ci bai ratsa jikinta gaba ki daya ba. shi yasa na gaggauta dawowa don na kira ka na sanar maka. sai kuma na ji jummai tayi dariya tana cewa eh dubu 50 ke na tunda na fadi wannan abun da ya faru ga hajiya. dan haka zan cigaba da lura da dukkanin abun da yake gudana ga hajiya da fatima da kuma Asmeer. sai ta kara cewa to zan kula sosai sir. tana gama fadan haka sai ta kashe wayar ta dawo wajena har da dafa ruwan zafin da tayi ta ce zata kawo miki don ta cigaba da kula da abun da yake faruwa haka dai muka tafo tare da ita. fatima tana zuwa dai dai nan sai ta fashe da kuka ta cigaba da cewa yanzu haka sunce yau din nan nazo da Asmeer ko su kashe ni, ammada nayi tunanin cewa baabata ba ta hanunsu sannan ban san halin da take ciki ba sai kawai na yanke hukuncin na sanar da ku dukkanin abubuwan da suke faruwa koda kuwa zasu kashe ni. tana zuwa dai dai nan sau wasu hawaye suka kara zubowa daga idanuwanta sannan ta cigaba da kuka sai kuma ke take cewa hajiya ku gafar cen bisa cin amanarku da nayi na son a kashe ku tare da taimakona. Tausayin fatima ne ya kama Hajiya da Asmeer da kuma doctor. hajiya rarrashin fatima ta shiga yi tana cewa "yata ki daina kuka ai ba ke kika aikata abun da ki kayi niyyar yi ba larai ce. sannan kuma dole aka miki don a miki barazana. sai dai kuma abun tambaya a nan shine: waye ya bige baabarki a mota? shin su waye wadannan azzaluman mutanen? waye ya saka su su kashe mu ni da dana? mi muka yiwa wanda yasa a aikata kisa a kanmu? babu shakka wadannan azzaluman mutanen ne suka je suka yiwa doctor baraza da dauke iyalinsa da suka yi don ya aikata mungun aiki a kaina don su cimma burinsu. [11:23PM, 5/26/2015] Asmeer: Da likita ya ji haka sai ya saki allurar da ke hannunsa ta fadi kas. sai ya ce tabbas babu makawa wadannan mutanen ne suka kama iyalina. da haka ya kamata mu gaggauta daukar mataki akan wannan al"amari dan ganowa waya saka su? miye burin wanda yasa a kashe ku? tare da sanin wanda ya buge baabar fatima. ya kamata muyi shawarar yanda za muyi mu sha kan wannan abun da yake faruwa tun kafin su gane cewa mun san komai. sai hajiya ta ce kwarai da gaske hakan ya kamata ayi tun kafin lokaci ya kure. shi kuwa Asmeer numfashi ya ja sannan ya ce babu mamaki wannan matar da na buge ita ce baabar fatima. amma yanzu abun da ya kamata muyi shine mu gaggauwa zuwa gurin da suke. sai hajiya ta ya ce ya za ayi mu dunguma muje gurinsu gaba daya ba zai yiwu ba. sai doctor ya ce to mi zai hana fatima ta je da Asmeer yaso ta ce ta kawo shi yaso sai ta saci jiki ta zo ta gaya mana mu kuma sai mu je da police. Fatima kuwa cewa tayi tabbas shawarar doctor ta yi sai dai kuma abun da ya kamata ayi shine mu je mu sanarwa police sai mu tafi tare da police din idan mun je kauyen sai police su tsaya a wajen da mutanen baza su gansu ba. sai ni da Asmeer mu karisa wajen, idan mun je wajen su saki jiki kamar sun samu abun da suke su. to su kuma daf da wannan lokacin sai police su je su kewaye gidan suyi attack nasu. Shawarar fatiman aka dauka sannan a lokacin likita ya sallami hajiya amma kuma sai suka ce hajiyan ta tsaya a nan asibitin, Asmeer da likita tare da fatima za su tafi police station su sanar mu sai su tafi can kauyen. hajiya kin yarda ta yi lallai sai an tafi da ita. sai Asmeer ya ce momi ki zauna a nan kinga baki da cikakkiyar lafiya. sai hajiya ta ce ai na warke. sai likita ya ce hajiya bai kamata ki je ba saboda har yanzu baki gama warkewa sosai ba. haka dai suka kai ta lallamar hajiya har ta hakura ta zauna. sai likita ya kira Nurse mace ya ce ta zauna tare da hajiya sannan ta mata dukkanin abun da hajiya ta bukata. fatima kuwa cewa ta yi to yanzu ya za ayi na je na ga matar da Asmeer ya bige ko ita ce baabata. sai Asmeer ya ce ki hakuri mu gama wannan abun da yake gaban mu. kar mu je hankalin waccar matar ya tashi. haka fatima ta hakura suka fita a asibitin suka nufin police station. a lokacin kuwa magarib da gabato haka dai suka nufi police station. bayan sun isa police station sai suka sanar musu halin da ake ci haka kuwa suka basu goyon baya bisa ganin hajiya ce da danta suka zo da kansu. domin kuwa sun san hajiya sosai ita da danta bisa shaharar da suka yi a garin game da bunkasar kasuwancin mijin hajiya. Ashe duk tattaunawar da su Asmeer su kayi da hajiya da fatima da likita tare da dukkanin bayanin da Fatima ta gaya musu a cikin dakin da aka kwantar da hajiya, Jummai tana jin su tana make a baki kofa tana rike da abincin da ta kawowa hajiya. koda ta ji motsin su Asmeer za su fita sai tayi wuf da buya a wani wajen da baza su ganta ba. bayan fitar su ne ta shi cikin dakin kanta a sunkuye tare da kebe kebe yanda zaka san munafuka ce. sai ta durkusa ta gaida hajiya. hajiya kuwa sai ta nuna kamar ba abun da ya faru sai kuma ta amsa mata da gaisuwarta kamar yanda ta saba amsa mata gaisuwa. sai ta karbi abincin ta ajiye a gefe. sai jummai ta tashi zata fita. sai hajiya ta ce ya daga zuwa zaki tafi? jikin jummai yana rawa ta ce eh zan tafi zan je mu karisa aikin da muke yi ni da sauran masu aiki. sai hajiya tayi murmushi ta ce to ayi aiki sosai yanda zan ji dadi biyanki albashi. jikin jummai sanyi yayi bisa jin abun da hajiya ta fada. amma haka ta fita da sauri ta nufi gidan hajiya. bayan fitar jummai a dakinne sai hajiya da batabrai ta ce "yar banza munafuka ai bazan ci abinci ba na daina yarda da ke kuma insha.Allah karshenku yazo ke da azzalumqn mutanen. sai kawai hajiya ta tashi ta je ta zubar da abincin. sai ta dawo tana ta tunanin irin makircin da ake hada mata ita da danta. kafin jummai ta karisa gidan hajiya da yake wayarta tana kunkuminta sai ta je ta samu wani lungu ta shiga tana waige waige alamar bata da gaskiya. bayan ta shiga lungun sai ta dannan lambar waya don tayi kira ta sanar abun da yake faruwa.R FATIMA ZAHRA novels / RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 22 RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 22 Posted by Bashir Sani Fesan on 28 Dec 2016 - 13:36 sai ta danna kira don ta sanar abun da yake faruwa. Bayan jummai ta gama waya sai tayi sauri ta bar wajen ta koma gidan hajiya. *** *** *** Fatima da Asmeer da likita da sauran "yan sanda bayan su karisa kauyen su fatima, sai aka tura Asmeer da fatima kamar dai yanda suka tsara abun su, su kuma police da likita sai suka taya a wani waje. haka Fatima da Asmeer suka doshi wannan gidan da azzaluman suke ciki. Tun kafin su shiga cikin gidan wanda ya saka azzaluman mutanen nan mungun aikin sai ya kira ogan azzaluman wato bakin arne ya sanar masa da su gaggauta barin gidan domin kuwa yanzu jummai ta kira shi a waya ta gaya masa cewa Asmeer da fatima tare suke da "yan sanda dan haka kar su yarda da su su gaggquta barin gidan. koda bakin arne ya ji haka sai yaki ya sanarwa yaransa saboda yana tsoron ya sanar musu wajen guduwa police su bude musu wuta su kashe su. don haka sai ya sulale ya bar yaransa ba tare da ya sanar musu ba. Bayan Asmeer da Fatima sun shiga gidan sai fatima ta saka Asmeer a gabanta ta fara cewa kuna ina ga Asmeer din ta kawo muku shi. sai da ta fada sau uku sannan yaran suka fito suka tsaya suna dariya, amma basu ce komai ba saboda suna jiran fitowar ogansu. sai da suka dauki lokaci mai tsawo suna jiran fitowar ogansu. koda suka ga ogansu bai fito ba sai suka umarci daya daga cikin su daya je ya duba lafiya kuwa har yanzu ogansu bai fito ba. koda suka duba basu ga ogannasu ba sai suka fara dube dube da mamakin rashin ganin ogansu. Asmeer da fatima suna tsaye suna ganin halin da yaran suka shiga. sai fatima ita ma ta fara mamakin rashin ganin ogan azzaluman wato bakin arne. suna cikin wannan halin ne sai suka jiyo a waje a lasifika ana cewa ku fito ku mika wuya cikin salama ba tare da kunyi gardama ba inhar kuwa kuka yi gardama zaku iya rasa ranku, domin kuwa police sun kewaye gidan nan ta ko ina ba ku da hanyar da za ku fita. koda yaran bakin arne suka ji haka sai suka kidimauce nan da nan jikinsu ya fara rawa. fatima kuwa cewa take yi ina kuka kai ogan na ku azzaluman banza azzaluman wofi? shiru suka yi ba su ce komai ba. haka dai azzaluman suka fito sun daga hannayensu sama suna muzurai, a cikinsu har da Larai ita ma hannayenta a sama. Bayan sun fito waje sai suka ga inspector na police tsaye a bakin mota. su kuma police sai sukayi attacking din azzaluman mutanen nan. sai wasu police guda biyu suka fito da ankwa suka sakawa dukkanin azzaluman. Likita kuwa cewa yake yi ai wadannan su ne wadanda suka je gidana suka min barazanar kisa inhar ba aikata abun da suka sakani ba na yiwa hajiya allurar mutuwa in ba haka ba za su kashe ni ni da iyalina. sai ya matso kusa da daya daga cikin azzaluman wanda shine ya angiza iyalansa zuwa motar su. sai ya je ya cakwamin kwalar rigarsa yana fadin ina iyalena? ina kuka kai su? sai wannan azzalumin yayi nuni da kansa alamar suna ciki. cikin hanzari likita ya shiga cikin gidan da gudu, sai daya daga cikin police ya bi bayan doctor. bayan sun shiga ciki sai likita ya shiga dube duben dakuna yana kiran sunan matarsa Habiba kina ina ke da muntasar da Amatullah wato "ya "yansa ke nan. koda ya ji shiru sai jikinsa ya fara rawa. ai kuwa suna shiga can wani daki wanda yake karshe likitan yana shiga sai ya ga matarsa da dukkanin "ya "yansa suna barci. hankalin doctor tashi yayi domin kuwa yayi tsammanin sun kashe masa iyalinsa, amma koda ya je ya taba matarsa da "ya "yan nasa sai ya tabbatar ba mutuwa suka yi ba haka ya tashe su daga baccin da suke yi amma sai ya ga babu wanda ya motsa sai ya tabbatar cewa kwaya aka ba su ko allura aka musu don suyi bacci. haka dai ya cincibi matarsa ya sakata a kafadarsa shi kuma police din wanda yake biye da shi sai ya dauki yaran likitan guda biyu ya sanya daya a kafadar dama dayan kuma a kafadar hagun har suka fito a cikin gidan. Bayan sun fito ne sai likitan da police suka sanya iyalen doctor a cikin motar da likita ya zo da ita. sai Asmeer da Fatima da sauran police suka tambayi doctor suka ce mi ya faru da iyalin naka sai ya ce musu sun ba su maganin barci ne ko kuma sun musu allura bacci, amma babu komai za su tashi idan na je na musu allurai. sai dukkanin su suka ce Ayyah! tunda babu wata matsala bayan haka Alhamdulillah. Ai kuwa sai inspector ya bada umarnin a saka dukkanin azzaluman a cikin mota a tafi. cikin cika umarni police din da suke wajen suka fara saka azzaluman a cikin mota. koda wata police mace ta je ta kama Larai zata sakata a mota sai Fatima ta zo wajen ta kalli Larai ta ce kinyi ta wallahi kin ci amanar matar da take kyautata miki, ki ci ki sha sannan ta biya ki albashin aikinki mai tsoka ga kyautata miki da take yi amma ki kasa saka mata sai da hada baki da ke dan a kasheta don abun duniya. dan haka ki gaggauta neman tubarta tun kafin ki bar duniya inhar baki nemi tubarta ba baza ki gama da duniya lafiya ba. daman hausawa sun ce makashinka yana tare da kai. Larai kuwa bata ce komai ba sai kawai ta kalli Fatima cikin halamun na dama. haka dai aka angiza Larai cikin mota. bayan an gama saka azzaluman a cikin mota mota sai dukkanin mutanen wajen suka shiga mota aka tafi aka doshi can cikin gari zuwa police station. [9:20AM, 5/29/2015] Asmeer: *** *** *** Shi kuwa bakin arne bayan ya sulale ya gudu ya bar yaransa a wannan gidan sai ya ratsa ta jeji ya ringa gudu har ya bar cikin kauyen ya je ya shiga cikin gari. kai tsaye gidan wanda ya saka su mungun aiki ya nufa. bayan ya je kofar gidan mutumin sai ya shiga cikin gidan kai tsaye da yake ya saba shiga, dan haka mai gadin gidan bai dakatar da shi ba. bayan ya shiga cikin falon gidan sai ya taras da shi yana zaune ya rike kansa yana tunani. Gidan kawatacce ne an gidana shi irin ginin zamani kamar gidan hamshakin mai kudi, an zuba duk wasu abubuwa na more rayuwa, a tsakar gidan wajen parking motoci kuwa mutoci hudu ne anyi parking din su duk an rufe su da tampol, a can gefe kuwa jeef ce prado a parking wacce ita ce mai gidan yake hawa, ta ko ina kuwa flowers ne kala kala a shuke sun kara kawata gidan. sai dai duk da kawatuwar gidan da yake da shi babu mace a gidan wato matar aure balantana a samu yara a gidan. Bayan bakin arne ya shiga cikin gidan koda mai gidan ya gan shi sai ya mike da sauri yana fadin ina fatan babu wata matsala? shi kuwa bakin arne zama yayi yana haki yana cewa tabbas akwai matsala domin kuwa na tabbata an kama dukkanin yarana. sai wannan mai gidan ya ce what? an kama su, ya akayi ka bari aka kama su alhalin na sanar makaFatima tare suke da police. sai bakin arne ya ce ranka dade nayi haka ne don na kubutar da kaina daga wajen police saboda na tabbata idan sun kamani za su tafi da ni idan sun tafi da ni kuwa za su ban azaba wacce zata yi sanadiyar bayyanar da wanda ya saka mu aikin, ka ga kuwa inhar na fada kai ka saka mu tabbas asirinka ya tonu sannan za a kamaka a rufeka kuma zaka tozarta, sannan inhar na gayawa yarana za muyi kokarin guduwa to kuwa inhar munyi kokarin guduwa police za su bude mana wuta to kuwa za mu iya rasa ranmu gabaki daya shi yasa na sulale na barsu domin kuwa ko motar mu ban hau ba da kafa na tako na zo ni nan. yana gama fadin haka sai wannan mai gidan ya zauna ya kalli bakin arne ya ce ai yanzun ma asirina da naka suna daf da tonuwa tunda an kama yaranka, ai dole su fadin wanda ya saka su inhar sun sha wahala. dan haka dole mu san matakin da za mu dauka. sai bakin arne ya gyara zama ya ce tabbas mu san yanda za ayi, idan ba haka ba asirin mu ya tonu. sai mai mai gidan yayi shiru sannan ya dafa kansa yana tunanin yanda za ayi. can zuwa wani lokaci sai bakin arne ya gyara murya ya ce to mi zai hana mu gudu mu bar garin kawai. sai wannan mai gidan ya dago da kansa ya kalli bakin arne ya ce baka da hankali ya za ayi mu gudu na bar tarin dukiyata a nan sannan duk inda muka je a fadin kasar nan sai an kama mu. sai bakin arne ya ce to miye mafita? sai wannan mai gidan ya kara yin shiru yana nazari. yana cikin nazarin sai ya ji wayarsa wacce ya wareta saboda kiran su bakin arne da sauran wanda ya saka su aiki domin kuwa babu wanda ya san lambar sai wanda ya saka aikin kashe hajiya da Asmeer. yana daga wayar don ya ga wanda ke kiransa sai ya ga lambar jummai. cikin rawar jiki ya dauki wayar sai ya ji muryar jummai kasa kasa tana cewa ranka dade za su kama ni fa domin kuwa ga nan su hajiya sun shigo gidan da police kuma ba ni da hanyar guduwa...tana gama fadan haka sai ya ji wayar ta yanke. sai ya ringa cewa jummai! jummai!! amma shiru. cikin sanyin jiki ya ajiye wayar. sai bakin arne ya ce mi ya faru da jummai? sai ya gaya masa. haka dai wannan mai gidan a shiga rudani can sai ya ce yauwa nasan yanda za ayi. sai bakin arne ya sau murmushi ya ce mi ke nan za kayi don mu kubuta sannan mu kubutar da yarana? sai ya kalli bakin arne ya ce tunda akwai kudi mi zai hana nasa mu daya daga cikin police na biya shi makudan kudi don ya sakawa yaranka da jummai da larai guba a cikin abincin da za a kai musu su ci su mutu ba tare da sun fadi wanda ya saka su aikin ba. sannan ka ga kaima hankalinka a kwance. yaso daga baya sai mu kara tsarin da za muyi don mu ga bayan hajiya da Asmeer har da Fatima. koda bakin arne ya ji haka sai ya kekece da dariyar mugunta ya ce tabbas haka za ayi. haka suka gama shirinsu na zuwa samun daya daga cikin police don ya aikata abun da mai godan ya yanke. Kashe gari kuwa da sassafe bakin arne da mai gidansa suka je suka samu daya daga daga cikin police a sirrance suka tura masa makudan kudi. " da yake yanzu rayuwa wasu basu da tsoron Allah ga son kudi" sai wannan police din ya yarda ya je ya sakawa yaran bakin arne guba a cikin abincin da aka kai musu. ba su dauki lokaci mai tsawo ba sai dukkaninsu su mutu. da yake lokacin an kai jummai an hada su ita da Larai sai su ma suka ci abincin mai dauke da guba wanda aka akawo musu cikin police station a cikin dakin da aka rufe su. bayan duk sun ci abincin sai suka mutu gabaki dayan su ba tare da sun fadi wanda ya saka su ba. inspector na police da ya ji mutuwar yaran bakin arne yayi bakin cikin sosai, nan da nan kuwa yasa a bincika masa wanda ya saka musu guba a cikin abincin. Hajiya da Asmeer tare da Fatima har da doctor suma sun ji bakin cikin mutuwar yaran arne saboda babu wanda za a bincika don a gano wanda ya saka a kashe hajiya da danta Asmeer. shi kuwa wannan police da ya saka guba a cikin abincin yaran bakin arne sai ya gudu ya bar garin ya tafi can wani gari gudun kar a gano shi ya zuba guba a ciin abincin. Bakin arne da mai gidansa kuwa murna sukayi kwarai da gaske ganin an kashe yaran bakin arne da su jummai. dan haka tun daga ranar suka fara sabon shirin na hanyar da za su bi su kashe hajiya da Asmeer da kuma FATIMA ZAHRA... ...tab! wannan shine an yanka ta tashi!!!.. ya ke nan? mu hadu a part 23. don jin cigaban wannan labarin.eer: <<> eer: <<>>Part 23. ....sai suka fara sabon shiri don suga sun kashe Asmeer da hajiya tare da Fatima zahra. *** *** *** A can gidan hajiya kuwa sai ya zamana ta canza salon zama da masu aikinta domin kuwa ta lura akwai masu munafurtatta. Fatima kuwa bayan sun dawo daga can kauyensu komai ya lafa sai ta bijirowa Asmeer game da maganar wacce ya buge a mota ya kaita asibiti, daman kuwa tun lokacin da ta ji cewa Asmeer ya buge wata mata a mota sannan yake kula da ita saboda ba a san "yan uwanta ba, shine hankalin fatima ya tashi tun daga wannan lokacin take son ta je ta ga wannan matar saboda jikinta ya bata ita ce baabarta. Bayan sun dawo daga can kauyensu ta samu Asmeer ta ke ce masa yayana ya kamata ka kai ni na je na gano wannan matar da ka buge a mota ka kaita asibiti don na dubata ko ita ce baabata. cikin murmushi Asmeer ya dubeta ya ce kanwata kar ki damu za mu je ki dubata, amma ki bari na je na siyo mata magun gunan ta aka bukaci na kai mata sai na zo mu tafi. sai fatima ta sau murmushi ta ce to mi zai hana mu tafi gabaki daya idan ka sayi maganin sai mu wuce ta can. sai Asmeer ya ce to shi ke nan mu tafi. Asmeeer ne ya fara shiga cikin dakin sai fatima ta biyo bayansa. koda suka shiga dakin sai suka taras da matar ta juya bayanta tana kwance. sai Asmeer ya zauna a gefen gadon da matar take kwance sai ya waigo ya kalli fatima ya ce ai matar ma tana barci. ita kuwa matar tana daga kwance ta ce idon biyu ban yi barci ba. sai Asmeer yayi murmushi sannan ya ce Ashe kin ji shigowar mu. sai matar ta ce eh ina jinku. sai Asmeer ya ce to ki yasa baki jiyo kin amsa zuwan mu. a lokacin kuwa Ashe kuka take yi Asmeer bai sani ba. koda ta ji tambayar Asmeer ba ta ce masa komai ba. Fatima kuwa koda ta ji matar ta yi magana sai jikinta yayi sanyi sai kuma hawaye ya cika idanuwanta saboda ta san baabarta bata magana don haka wannan matar ba baabarta ba ce saboda baabarta bata magana. koda Asmeer ya ga halin da fatima take ciki sai ya dubeta ya ce kanwata Fatima Zahra mi ya sakaki cikin wannan halin? ita kuwa matar da take kwance koda ta ji Asmeer ya ambaci fatima zahra sai ta yi wof ta juyo don ta ga wace ce fatima zahra da Asmeer ya ambata domin kuwa akan ta daman take kuka. Ita kuwa Fatima koda Asmeer ya tambaye ta dalilin da yasa hawaye ya cika idanuwanta. sai kawai fatima ta fita a dakin tana kuka ba tare da ta ga fuskar matar ba. Asmeer sai ya bita a baya cewa mi ya faru Fatima kike kuka? bata kula shi ba ta je ta bude motar da suka zo da ita ta shiga ta cigaba da kuka. ita kuwa matar da ke kwance a kan gado bayan ta waigo sai ta ga wannan wacce Asmeer ya kira da fatima zahra ta fita daga dakin tana kuka. sai matar ta mike ta zauna tana zubar da hawayen domin kuwa bata da ikon da zata tashi ta bi bayan su Asmeer sakamakon raunukan dake jikinta, dan haka sai ta cigaba da tunanin "yarta fatima wacce aka raba ta da ita domin kuwa tana tsammanin ma sun kasheta saboda sun ce inhar ba ta aikata abun da suka umarceta ba za su kashe ta. shi yasa akoda yaushe take kuka tana tunaninta. duk wannan kuka da tunanin da take yi Asmeer bai sani ba. Asmeer bayan ya je ya samu fatima a mota tana kuka sai tambayeta dalilin da yasa ta fito tana kuka? bata bashi amsa ba ta cigaba da kuka tana cewa ba ita ba ce baabata. wayyo! Allah na. koda Asmeer ya ji abun da fatima ta ce sai ya cika da mamaki amma sai ya gagara magana. fatima bata gushe ba ta cigaba da kuka tana cewa yayana ka miyar da ni gida. shi kuwa Asmeer jikinsa a sanyaye. ya dubeta ya ce kanwata baki gaya min dalilin kukanki ba. sai fatima ta ce ka mai da ni gida zan gaya maka idan mun koma gida. haka dai Asmeer ya shiga mota ya tuka suka nufi hanyar gida. ba tare ya je yayiwa matar sallama ba. [1:23PM, 5/31/2015] Asmeer: Bayan sun dawo gida sai Asmeer yake tambayar fatima dalilin da yasa take kuka? sai fatima ta ce masa wannan matar da muka je wajenta ba ita ba ce baabata saboda ita baabata bata magana. sai Asmeer yace mata eh gaskiya wannan matar kuwa tana magana. domin kuwa tun lokacin da aka gama mata aiki a asibiti da ta dawo hayyacinta na ji tayi magana. sai fatima ta ce to ka ga kuwa ba baabata ba ce. sai Asmeer ya ce to ai da kin tsaya kun gaisa kika sani ko ita ce Allah ya bata lafiya ta fara magana. sai fatima ta ce hmmm..baabarta wa da anyi mata magani har an ga ji. sai Asmeer ya ce to ai Allah mai iko ne akan komi nasa. dan haka ki daure mu koma ku gaisa. sai fatima ta ce a"a bazan koma ba. haka dai Asmeer ya dage lallai ta je ta gano ko ita ce. Amma sam fatima taki yarda. a dole ya hakura. shi kadai yake zuwa wajen wannan matar ya mata hidima ba tare da fatima ta je ta ba. ita kuwa fatima ta kasance cikin halin damuwa na rashi baabarta domin kuwa ko a talabijin ko gidan redio ko a jarida bata ji ana cikiyarta baabarta ba. sai ya zamana ta kasance cikin damuwa da tunanin baabarta. hajiya kuwa kullum tana rarrashinta tana bata hakuri kan cewa inhar baabarta tana raye babu shakka wataran za su hadu. hakan ya san fatima ta rage damuwa. Kamar duk wata yanda hajiya ta saba zama a can wani kawataccen gidan don biyan ma"aikatanta yau ma haka ne sai dai kuma wannan watan a gidanta akayi taron saboda wasu dalilai nata. Bayan an gama fitar da dukkanin ribar da aka samu a wannan watan sannan ta ware kudaden da ake biyan ma"aikatanta na gida da na sauran kamfanoninta. Bayan ta sallamin kowa sai ta dakatar da babban manajanta ta ce masa ya dakata akwai maganar da take so suyi. Bayan manajan ya zauna sai hajiya ta dube shi ta ce masa yauwa manaja na daman kamar yanda na maka alkawari zan biya maka kudin saudiya kamar yanda na saba duk shekara to wannan shekarar ma zan biya maka kai da yayarka. sannan na kara maka albashi akan na da, ina biyanka naira million biyu duk wata to yanzu zan ringa biyanka naira million biyar na kara maka million uku ke nan. baya ga haka akwai sabon gidan da na gama ginawa a nan kusa da mu to na bawa yayyarka. koda manaja ya ji irin kyaututtukan da hajiya ta mishi sai yayi godiya kwarai da gaske har da zubar da hawaye. sai hajiya ta ce haba! manaja ai wannan ba abun kuka ba ne ka cancanci na maka dukkanin wadannan abubuwan bisa rike dukiyar mijina amana da kake yi tun yana raye har ya zuwa yanzu. sai manaja ya ce dole nayi kuka ai bisa wannan alkairi da kika min babu abun da zan ce miki sai dai na ce Allah ya saka da alkairi ya kara bunkasa kasuwancinki ya kuma kare ki daga dukkanin mahassadanki. Sai hajiya tayi murmushi sannan ta ce Ameen. sai hajiya ta ce sai dai kuma har yanzu ba ka kara aure ba tun rasuwar matarka tafarko baka kara aure ba. sai ya sukuyar da kansa cikin kunya ya ce eh ina shirye shirye. amma zanyi insha"allah. sai hajiya ta ce ko dai kana so na nema maka wata bazawara ce? sai ya saka dariya ya ce haba! hajiya ki bari kawai zan nema da kaina na fi son na auri budurwa saboda yanzu an daina yayin bazawara. sai hajiya ta saka dariya ta ce an daina yayinmu, sai ya ce a"a ai ba ke nake nufi ba. sai ta ce har nima mana tunda nima ina jerinsu, to bari ka ji bazawarorin sun fi akan "yan mata. sai manaja ya sa dariya ya ce hajiya ke nan. sai ta ce hajiya ko gaskiya. sai manaja ya sunkuyar da kansa yana murmushi tsabar kunya. sai ya ce to hajiya ni kam zan tafi. sai ya mike da nufin tafiya sai hajiya ta ce af ban gaya maka abun da ya faru da ni da dana ba da kuma fatima. sai manaja ya dawo ya zauna ya ce mi ya faru da ku?sai hajiya ta nisanta ta ce nasan baka san abubuwan da suka faru da ni ba da kuma abun da aka shirya mana ni da dana Asmeer na kashe mu da aka yi niyar yi. saboda kai a lokacin ka ce min ka tafi kwatano duba kayayyakina na can. A fusace ya ce kashe ki kuma hajiya ke da danki da fatima wacce kike son ta zama sirukarki? sai hajiya ta ce eh. sai ya ce mi ya faru haka? sai ta kwashe dukkanin abubuwan da ya faru da zayyana masa. ai kuwa yana ji sai kawai.ANKO BOOKS [8:43AM, 6/2/2015] Asmeer: <<>>Part 24. ...Ai kuwa yana ji sai kawai ya ce hajiya abubuwan da suka faru da ke ke nan, to amma an gano wanda ya saka a aikata hakan kuwa? sai hajiya ta ce A"a ba a gano ko waye ba amma police suna bincike. sai manaja ya ce tabbas mahassadanki ne suke kokarin ganin bayanki don su ga sun mallake dukiyar da kika tara, yanzu abun da yafi shine zan samu miki masu tsaronki suna kula da lafiyarki. sai hajiya ta ce ai an kawo min police guda biyar masu kula da lafiyata da na dana da fatima. sai manaja ya ce to amma ya akai ban gansu ba? sai hajiya tayi murmushi ta ce akwai guda daya biyu a waje sauran kuma sun raka su fatima da Asmeer super market. sai manaja ya numfasa ya ce kwarai kuwa da zan shigo na ga police guda biyu sai da suka caje ni tukun na shigo nan. sai hajiya ta ce ai mutanan da suke kokarin ganin bayana insha"allah ni zan fara ganin bayan su domin kuwa akwai wani shiri da nake yi akan su yanda zanyi saurin gano su. a firgice manaja ya ce wani irin shiri kike yi akan su hajiya? ganin yanda manaja ya firgita ya bawa hajiya mamaki sai ta dubi manaja ta ce ya naga ka firgita haka? lafiya kuwa? cikin sunkuyar da kansa ya ce a"a babu komai kawai jin cewa akwai shirin da kike yi ne akan mutanan nan ne abun ya ban mamaki saboda kina mace har akwai abun da za kiyi alhalin ga mu nan muna nan mu ya kamata mu dauki matakin ganin bayan azzaluman mutanen nan. sai hajiya tayi murmushi ta ce haba! manaja na kasan na yarda da kai sosai dan haka ba zan iya 6uye maka komai ba game da abun da yake faruwa a gare ni. sai manaja ya murmusa ya ce haka ne hajiya. sai hajiya ta dago da kanta ta ce kasan dana yana daf da auren fatima sannan ya daina shaye shaye ya nutsu don haka yana yin auren zan mika masa komai na kasuwancin mahaifinsa shi zai ringa juyawa sannan shi zai ringa biyan ma"aikata albashi da dai sauran kulawa da dukkanin dan kasuwa yake bawa kasuwancinsa. sannan daman ba wani abu nake shiryawa wadanan mutanen ba illah... kafin ta cigaba sai ta ji sallamar Asmeer da fatima sun shigo. cikin murmushi hajiya ta dauke hankalinta daga kan manaja ta kalli fatima da Asmeer ta ce sannunku da dawowa "ya "yana. sai dukkaninsu suka ce yauwa hajiya. wani irin kallo Asmeer yayiwa manajan hajiya, koda manaja ya ga irin kallon da Asmeer ya saba yi masa cikin sauri ya sunkuyar da kansa da yake daman Asmeer ya saba yi masa irin wannan kallon mai dauke da Allah wadaran. Domin kuwa Asmeer yasan munanan halayen manaja wanda hajiya bata sansu da shi ba domin kuwa manaja ya saba zuwa gidan karuwai ya debowa karuwai yana lalata da su a gidansa, sannan kuma Asmeer ya sha ganin manaja a gidan giya da wajen caca. amma manaja bai taba ganin Asmeer a irin wannan guraren ba sai lokacin da wata karuwa ta zo wajen Asmeer yana zaune a wajen da yake shan giyarsa sai karuwar ta zo ta zauna kusa da Asmeer take ce masa ranka ya dade tun ba yau ba nake son yi maka magana ina tsoro sai yau domin kuwa na dade ina sonka. sai Asmeer ya daka mata harara ya ce ke ni duk iskancina ba na bin matan banza. sai wannan karuwar ta ce eh na ji amma ka yarda da ni ko sau daya. A fusace Asmeer ya mike ya kalleta ya ce mata na ce miki ni bana hulda da matan banza ki hanzarda barin nan wajen ko na wulakantaki. sai wannan karuwar tayi masa wani irin kallo mai dauke da ka tausaya min. sai ta rike rigarsa tana cewa ka taimaka min kazo muje jost sau daya ne fa. cikin 6acin rai Asmeer ya mike tsaye ya dauki hannunsa ya gaura mata mari ji kake tassss...sai da kowa wanda yake wajen ya kallo wajen to a lokacin kuwa manaja yana zaune a ta bayan Asmeer bai san Asmeer ba ne sannan kuma karuwar da ya mara yarinyar manaja ce don haka a fusace manaja ya taso ya rike rigar Asmeer ta baya sannan ya dauki hannu zai kaura masa mari. ai kuwa manaja yana arba da fuskar Asmeer sai ya saki rigar Asmeer take a wajen jikinsa ya fara karkarwa. shi kuwa Asmeer yana ganin manaja ne ya rike rigarsa ta baya har yana kokarin marinsa sai kawai ya kalli manajan kasa da sama bai ce masa komai ba sai kawai ya fice a bar wajen. ita karuwar da ta ga Asmeer ya fice ya bar wajen. ita kuwa karuwar sai take cewa manaja pls ka taimaka min ka je ka dawo min da waccan guy din ina son shi wallahi. manaja a fusata yayi agame da abun karuwar ta ce sai kawai ya gaura mata mari ya ce baki da hankali ne kin san ko shi waye? hada rai tayi ta ce oho ko shi waye ina son shi. ran manaja kara baci yayi sai kawai ya daka mata tsawa ya ce kin cuceni kika saka na zo na kusa na marin dan uwar gidana. sai kawai karuwar ta ce malam daina min tsawa. ina ruwana ko shi waye a wajenka. sai kawai manaja ya fita a wajen bai kara dawowa wajen ba. To shine tun daga ranar bai kara dawowa wajen ba sannan yake jin kunyar Asmeer sosai. shi kuwa Asmeer babu abun da yake cewa manaja sai harara kawai. ko sako hajiya ta bawa Asmeer ya kaiwa manaja sai dai kawai ya kai masa babu wata magana da take shiga tsakaninsu. sai ya zamana manaja yana tsoron Asmeer sosai. sai dai abun da yayiwa manaja dadi shine abun da ya faru a tsakaninsu bai gayawa hajiya ba. da ya gayawa hajiya tabbas da yaga canjin fusaka a wajen hajiya. [9:43AM, 6/3/2015] Asmeer: wannan shine dalilin da yasa duk lokacin da Asmeer ya kalli manaja sai ya daka masa harara. shi kuma manaja sai ya sunkuyar da kansa. ita kuwa hajiya bata taba lura da abun da yake gudana a tsakanin Asmeer da manaja ba. Bayan Asmeer ya wuce ya shiga daki. ita kuma fatima zata wuce sai da ta durkusa ta gaida manaja don girmamawa. Manaja kamewa yayi da ya ji irin sautin muryarta. domin kuwa sai yanzu ne ya saurari sautin fatima mai rikirkita kunnuwa, bai taba miyar da hankali ya saurari sautin muryar fatima ba sai wannan karon, ai kuwa sai ya ji kirjinsa ya buga da karfi. Hajiya ce ta masa magana sannan ya dawo hayyacinsa. sai hajiya ta dube shi ta ce babban manajana lafiya kuwa naga ka kidimauce haka? kikinar dole ya fara yana cewa aaaa"aaaa babuuuu komai hhhhajjjjiya. sai hajiya ta yi murmushi ta ce ka fada mana akwai abun da ke damunka. mikewa yayi daga kan kujera ya ce ni kam zan tafi hajiya na gode sosai da alkairan da kika min. sai hajiya ta tashi ita ma tana cewa babu komai babban manajana ai komi na maka ka dace a maka hakan. har manaja ya fita a falon gidan godiya ya ke yi. haka dai ya fita ya je ya shiga mota ya bar gidan. *** *** *** Batun matar da Asmeer yake kula da ita a asibiti kuwa haka Asmeer ya cigaba da bata kulawa har ta samu lafiya. bayan ta samu lafiya sai aka sallameta sai Asmeer yake tambayarta yanzu ya za ayi game da komawarki gidanku? sai matar take cewa ita bata da kowa a garin nan, sai dai kuma akwai wani kauye gabas da garin nan wanda a akwai gidan wata mata wacce nake zama a gidanta. sai Asmeer yake cewa to ko kin san sunan kauyen sai ta ce eh na ji dai ana cewa kauyen katsinawa. sai Asmeer ya ce au anan kauyen kike? kinga kuwa kwanan nan mukayi wani kes a chan. ashe a nan kauyen kike? sai ta ce eh amma kuma ina tsoron komawa saboda akwai wasu azzaluman mutane da za su iya su kamani. abun da matar ta fada ya bawa Asmeer mamaki sai dubi matar ya ce wasu mutane ne haka? sai matar ta ce eh ai kasan tun da ka kawo ni wannan asibitin ban taba gaya maka labarina ba da kuma abun da ya same ni. sai Asmeer ya ce eh haka ne. sai matar ta ce yanzu dai babu lokacin da zan baka labarina sai mun samu waje. sai Asmeer ya ce to mi zai hana mu je gidanmu na kai ki ku gaisa da mahaifiyata. sai matar ta ce gaskiya ne dan kuwa ina so na ce maka ka kaini wajen mahaifiyarka na mata godiya bisa kyautatawar da take nuna min. sai Asmeer yayi murmushi ya ce ai mahaifiyata tana tausayin duk mutumin da yake cikin wani hali na tausayawa. sai matar ta ce Allah sarki gaskiya yi sa"ar mahaifiya. sai Asmeer ya sau murmushi sannan ya ce sai ki zo muje mu shiga mota mu tafi. haka matar ta bi Asmeer suka je suka shiga mota suka nufi gidansu Asmeer. *** *** *** A can bangaren su bakin Arne da maigidansa kuwa cigaba suka yi da tarkon Asmeer da hajiya. sai mai gidan bakin arne ya zo ya samu bakin arne yake ce masa kai jiya fa na je gidan hajiya na jiyo wasu abubuwan da ya tayar min da hankali sannan kuma zuciyata ta tafo da son wata yarinya da ta rkirkita min zuciyata wanda inhar ban mallaketa ba zan iya shiga wani hali. baya ga haka inhar ba mu tashi mun kashe hajiya da dan taba ina daf da rasa matsayina da nake da shi a wajen hajiya domin kuwa dukkanin wasu harkokin kasuwancinta na nan Nigeria da na kasashen zata damkasu ga danta Asmeer. inhar ta damkasu ga hanunsa kuwa tawa ta zo karshe sannan kaima baza ka samu abun da na ce maka ba. dan haka dole mu hallaka hajiya da Asmerr cikin kwanaki kalilan. koda bakin arne ya ji haka sai ya mike yana huci yana cewa mai gidana a yau dole hajiya da danta har da wannan yarinyar su bakunci lahira. ta shi yayi cikin sauri ya ce baka da hankali ne za ka ce har da wannan yarinyar wato fatima wacce yanzu ta zamo min mahadar rayuwata. sannan na ji ka ce yau za a kashe hajiya da danta to ka sani akwai "yan sanda tattare da ita da Asmeer dan haka dole mu mu san hanyar da za mu bi mu kashe su ba tare da police son sani ba kuma nan da sati ya kamata mu gaba bayan su...AHRA novels / RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 25 RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 25 Posted by Bashir Sani Fesan on 28 Dec 2016 - 13:46 nan da sati ya kamata mu ga bayansu. bakin harne huci yayi tamkar ya ci babu ya ce mai gida an gama, sannan nan a yau din nan zan hada sababbin yara wadanda za muyi aikin da su, amma shin so kake a shiga har cikin gidan hajiya a kashe su ko kuwa kafi son a tare su a hanya a kashe su? Shin da bindiga kake so a harbe su ko kuwa yankan rago kake so ayi mu su? koda ya ji haka sai ya ce babu ko daya, yanzu dole mu san hanyar da za mu gama da su ba tare da wata matsala ba kuma ba tare da an san ni na kashe su ba, kuma dole nasan hanyar da zan bi na mallaki fatima ko ta yaya. sai bakin arne ya ce ai mallakar fatima mai sauki ne mai gida, kai dai ka kwantar da hanlinka tamkar ka mallaki dukkanin abun da kake so. tun tsurewa yayi da dariya sanan ya dubi bakin arne ya ce shi yasa nake son na sakaka aiki saboda baka da tsoro kuma baka da imani. sai ya saka hannunsa a aljihu ya fiddo da bonch din dubu dubu ya mika masa ya ce ga wannan ka je ka nemo wanda za kuyi aikin. koda bakin arne ya ga wannan dubin kudin a hannunsa sai ya kece da dariyar mugunta ya ce sai mai gidana tabbas duk wanda zai ma aiki dole yayi cikin gaggawa saboda kana sake hannu. sai bakin arne ya fiddo da sigari ya bunka mata wuta sannan ya zuka ya busa hayakin a saman silin falon, sannan ya juya ya fita yana cewa mai gida sai na dawo. sai ya ce yauwa ina jiran ka fa. kafin ka dawo zan san ta yanda za a kashe hajiya da danta sannan na mallaki FATIMA ZAHRA. *** *** *** Asmeer da matar da ya taimawa shigowa cikin falo suka yi tare da sallama, amma da yake babu kowa a cikin falon babu wanda ya amsa musu sallamar. bayan sun shigo sai Asmeer ya nunawa matar kujera ya ce mama ga waje ki zauna bari na je na kira momina tana ciki. cikin murmushi ta ce to dana. sai matar ta zauna. zaman da tayi ne akan kujera zai tabbatar maka bata saba zama a irin wannan kujera ba, zaman ta ke da wuya sai ta fara kalle kallen falon tana ganin irin kawatuwar da yayi da kuma irin abubun da aka saka a cikin falon, kai ka ce gidan governor ne. sai kawai matar ta rike baki ta ce 0 wannan ai ita ce aljannar duniya sai ka ce ba a duniya ba. kai Amma masu kudin suna jin dadi. uhm! Allah mai azurta wanda yaso sannan ya talautar wanda yaso cikin ikonsa da adalcinsa... Tana cikin wannan kale kalen da mamaki sai ta ji hajiya ta ce sannunki da zuwa. cikin murmushi ta ce yauwa hajiya. sai hajiya ta je ta bude firij din dake cikin falon da dakko 5alive mai sanyi sannan da dakko wani plate da kofi daga cikin firij din ta kawo gaban matar, da kanta hajiya ta bude lemon ta zuba a kofi tana cewa Ashe ke ce matar da dana ya biga da mota? sai matar ta ce eh nine wallahi. a dai dai wannan lokacin ne hajiya ta gama zuba mata lemon a kofi sannan ta ajiye a gaban matar.sai hajiya ta ce gashi ki kashe kishirwa. cikin kunya ta ce to nagode kwarai da gaske sai ta dauki kofin wanda yake dauke da lemon. sai ta sha sannan ta ajiye guntun. sai hajiya ta dubeta ta kara cewa jiki yayi karfi sai matar ce Alhamdulillah jiki ya warware. sai hajiya ta ce haka ake so. sai matar ta ce daman godiya na zo na miki bisa alkairin da kika min na aiko min da magun guna da abinci da kuma dawainiyar da danki ya min. sai hajiya ta yi murmushi ta ce Ayyah ai babu komai. shi kuwa Asmeer bayan ya je ya gayawa hajiya sai ya je ya hau matakala ya nufi dakin Fatima. koda ya je bakin dakin sai ya kwankwasa tare da kiran kanwata...ita kuwa fatima a lokacin barci ta ke yi. shi kuwa Asmeer bai gushe ba ya cigaba da kwankwasawa yana cewa kanwata kina ina ne kizo ki bude. hajiya tana daga can kasa sai ta jiyo kiran da Asmeer yake yiwa fatima sai ta ce masa barci da take yi dazun nan muna kallon news ta shiga dakin ta ce barci take ji ka barta tayi barcinta ta huta. koda Asmeer ya ji haka sai ya sakko yana fadin kash! ai na so ta zo ta gaisa da matar nan. haka ya sakko ya dawo wajen da hajiya suke zaune. a lokacin kuwa matar ta gama yiwa hajiya godiya. dan haka lokacin da Asmeer ya zo sai ya cewa matar yauwa wannan ita ce momina. sai matar ta ce ai mun gaisa. sai Asmeer ya ce ai naso ku gaisa da kanwata ma sai kuma gashi tana barci. sai matar ta ce Ayyah ai bakomai. sai Asmeer ya nisanta ya ce yauwa daman kin ce sai mun zo nan zaki ban labarinki. hajiya cewa ta yi Laaa! ka ji min dan nan ya za ka ce ta baka labarinta? sai matar da sau gutun murmushi ta ce aaa bakomai hajiya ai ni na ce zan gaya masa. sai hajiya ta ce to naga bai kamata ya ce sai ya ji labarinki. sai matar ta ce kar ki damu hajiya nima na ji dadin tambayar da ya min. sai hajiya ta ce to shi ke nan sai ki gaya masa labarinki. ita kuwa fatima tana cikin barcinta sai take mafarkin baabarta ta ringa mafarke mafarke marasa ma"ana akan baabarta. a firgice ta tashi tana salati. tana farkawa kuwa sai ta jiyo maganganu daga cikin falon. cikin sanyi jiki ta mike da je ta bude kofar dakinta a hankali don ta leka su waye da waye a falon. ai kuwa tana lekowa sai tayi arba da fuskar baabarta. [9:22AM, 6/5/2015] Asmeer: ji tayi kirjinta ya buga da karfi. sai kuma ta fara murtsuka idanuwanta tana cewa mafarki nake yi ne ko kuwa gizon baabata nake gani. da ta ga dai da gaske baabarta ce sai kawai ta bude kofar dakinta da sauri ta sakko kasi, tana kiran baaba! baaba!! baaaba!!! tsabar murta da saurin da take yi sai da ta fadi a kan matakalar, jin faduwar da tayi ne Asmeer da hajiya suka juyo da sauri, ita kuwa baabarta ta bude bakinta ke nan za ta bawa su Asmeer labarinta sai ta jiyo kiran da fatima take mata da kuma faduwar da tayi, koda ta waiga ta ga fuskar fatima sai ta mike da sauri ta je ta daga ta daga faduwar da tayi. Fatima tana ganin. baabarta ce ta dagata sai ta rungumeta tana kuka tana cewa baabata daman baki mutu ba. sai itama hawaye ya kwararo daga idanuwanta tana cewa ban mutu ba "yata. Asmeer da hajiya kuwa tashi suka yi daga kan kujera suka tsaya suna mamakin su fatima da baabarta, ganin yanda suke zubar da hawaye ne da zantukan da suke fada shi ya bawa su Asmeer tausayin fatima da baabarta sai suma hawaye ya cika idanuwansu. *** *** *** A can ban garen bakin arne da mai gidansa, bayan bakin arne ya nemo yaran da zai yi aiki da su sai suka zauna suna tattaunawa irin kisar da za suyiwa hajiya da danta. sai wannan mutumin wanda ya saka bakin arne aikin kashe su Asmeer sai ya ce na gano hanyar da za a bi don kashe Asmeer da hajiya cikin sauki, amma kafin ku kashe hajiya sai kun kawo min ita nan gidana ta sai na kawo mata file din da suke guna na babban kamfaninta ta saka hannu sannan ta dakko min duk sauran file din kamfanoninta na nan kasar da na kasashen waje ta saka hannu, baya ga haka sai ta saka hannu a cheque din bankunan da ake ajiye kudaden kamfanoninta, idan ta gama saka hannu kaf sai na kasheta da hannuna sannan na baku gawarta ku je ku jefa a cikin kogi ko ku binneta a wajen da baza a ganku ba. amma kafin kuna kawo min hajiya za ku je ku kama Asmeer ku kashe shi ko ku kawo min shi sannan ku tafo min da fatima. koda bakin arne ya ji haka sai ya ke ce da dariyar mugunta sannan ya ce to ya za muyi da police da suke kula da hajiya da danta? sai wannan wanda ya saka bakin arne aikin sai ya ce su kuma police yanda za a musu shine, kai bakin arne za kayi badda kama ne ka je wajen police da suke kula da hajiya ka ce musu kai daya daga cikin yaran da kuka kayi kokarin kashe hajiya da Asmeer ne sannan kuka kama iyalan likita sai ka ce masa tun kafin police su zo su kama wadanda suka yi kokarin kashe Asmeer da fatima a lokacin da fatima ta kawo Asmeer kuka samu sabani da oganku ka tafi, dan haka kazo ka kaisu wajen wanda ya sakaku ku kashe Asmeer da kuma hajiya to a lokacin za suyi kokarin su kira wasu "yan sanda akan su zo su je tare da su. to kai kuma sai kace masu a"a kar su kira kowa saboda wanda ya saka su yana target din duk wani motsin police dan haka sai su biyo ka ka kaisu, amma sai ka ce musu su cire uniform din su kar wani daga cikin masu lura da motsin police ya gansu, to inhar ya ganku to zai gayawa mai gidanmu. to idan ya gaya masa kuwa zai sa a kashe ku ta yanda ba kuyi tsammani ba. to kana gaya musu haka za su je su cire uniform na su su bika don su je su kama wanda ya saka a kashe hajiya da dansa, domin kuwa duk police suna neman wanda ya saka a kashe hajiya da danta don su samu karin girma. to kai kuma sai ka kaisu can bayan gari ka summace su ka kashe su. to ka ga an gama da police masu kula da hajiya, yaso sai kuje har cikin gidan hajiya ku kamo min ita ku kawo min ita gidana, cikin sauki.amma fa ba da irin shigar nan za kaje wajen police din da shi ba, kaya masu datti zaka saka yanda zasu tabbatar eh kayi kama da mutanen da suka kama a can kauyen su fatima. police masu kula da Asmeer da fatima kuwa da yake duk bayan sallar la"asar idan rana tayi sanyi Asmeer yaka dauki fatima a sabuwar motar da hajiya ta siyawa fatima suna zuwa can filin jirgi yana koya mata mota to sukan tafi da police guda biyu don kula da lafiyar Asmeer da fatima. to sai ku bari sai suna dawo daga filin jirgin idan za su koma gida sai ku tsayar da su. suna tsayawa idan police sun fito sai ku bude musu wuta da bidigogin da zan siya muku, amma shiga za kuyi irin ta miskinai kamar masu neman taimako, to idan kun je kun tsayar da motar su Asmeer din sai kuna cewa fisabilillah! to Asmeer yana da tausayi zai tsaya don ya baku sadaka su kuma police din za su fito don suyi muku masifa su ce ku bar wajen. to ku kuma police din suna fitowa sai ku fito da bindigoginku ku harbe su.bayan kun harbesu sai ku tafo min da Asmeer da fatima nan gidana. sai na hada Asmeer da maifiyarsa na kashe su da kaina ita kuma fatima na mallaketa. amma fa ba a cikin gari za ku tsayar da Asmeer ba a"a a can bayan gari za ku tsayar da su da yake ta bayan garin suke bi. koda bakin arne da sauran yaran suka ji haka sai suka sa ihu suna cewa kai mai gida kana da brain, ai idan ba mai kwakwalwa ba ba yanda mutum zai sai irin wannan hanyar da za abi a kashe hajiya da Asmeer cikin sauki. sai ya dubesu yana murmushi ya ce to yanzu dai gobe za ku je kuyi wannan aikin. sai suka ce mi zai hana yanzu. sai ya ce musu a"a banda yau kam ai yanzu dare ya gabato aikin ba zai yiwu ba. haka da suka kece da dariyar muguta suna cewa gaskiya ne. sai mai gidan nasu ya dakko wani plask wanda siyo abinci a restaurant, da kansa ya shiga kitchen ya dakko plate da kofuna sannan ya dakko joice a cikin firij ya kawo ya zubawa kowa sannan suka hau ci suna hirar kashe Asmeer da hajiya da kuma yanda za su kawowa mai gidansu LOGIN 53 0 68 13 9 6 37 31 40 1 2 2 1 63 3 55 28 8 30 0 51 fufore, adamawa, nigeria Bashir Sani Fesan ♥ Home / RAYUWAR FATIMA ZAHRA novels / RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 26 RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 26 Posted by Bashir Sani Fesan on 28 Dec 2016 - 13:50 yadda za su kawowa mai gidansu FATIMA ZAHRA. *** *** *** A can gidan hajiya kuwa lokacin da Fatima ta rungume baabarta tana kuka sai Asmeer da hajiya suka cigaba da tausayawa fatima da baabarta. can zuwa wasu lokuta sai baabar fatima ta janye jikinta daga jikin fatima sannan ta kalleta a lokacin da hawaye yake zuba daga idanuwata sai ta ce godiya ta tabbata ga sarkin da baya barci, mabuwayin kowa da komai, Allah nagode maka da ka hada ni da "yata wacce koda yaushe nake zubar da hawaye saboda ita. yau ga ni ga ta sai hawaye ya kara kwararowa daga idanuwanta. Fatima kuwa gogewa baabarta hawaye take yi tana cewa ki daina zubar da hawaye tunda gani a gare ki, sai ta kama hannunta ta je ta zaunar da ita kusa da hajiya, ita ma a lokacin hajiya ta zauna. sai fatima ta kalli hajiya ta ce hajiya wannan ita ce baabarta wa wacce na sanar da ita a gare ku, sai hajiya ta murmusa ta ce Allah sarki. sai fatima ta kara duban baabarta ta ce baaba amma abun mamaki shine naga kina magana alhalin da baki magana. sai baabar fatima ta ce haka ne kam sai ta gyara zama ta dubi fatima ta ce tabbas da ba magana Amma yanzu cikin ikon Allah ina magana bisa taimakon addu"o"i da kuma taimakon likita. sai fatima ta ja numfashi sannan ta kara kallonta ta ce to amma ya aka yi kika kubuta daga sharrin azzaluman mutanan nan? sannan kuma da irin taimakon da likita ya miki har kika samu lafiyar rashin maganar da kike yi? sai baabar fatima ta ce lokacin da wannan azzaluman mutanen suke tattaunawa yanda zasu kashe ni ne a can wani daki. su basu yi tsammanin ina jin magana ba saboda sun ga lokacin da kike min magana bana miki magana dan haka sai suka yi tsammanain ni kurmiyace bana magana. dan haka sai suke tattaunawar yanda zasu kashe ni. ni kuwa ina jinsu sai kawai na tashi na bi ta taga(window) na gudu. duk galabaitar da nayi na rashin abinci da kuma damuwa bai sa na gagara guduwa ba saboda tseratar da raina. haka na bi ta cikin jeji ina gudu ban ankara ba sai na ga azzaluman mutanan nan suna bina suna cewa na tsaya idan ba haka ba, inhar sun kamani kashe ni za suyi. ni kuwa gudu na cigaba da yi ina neman taimako. to bayan nayi gudu mai nisa wanda ni kaina ban san adadin yawan nisan dayi ba sai kawai na fara gajiya tare da nishi tamkar kirjina zai fito, amma haka na daure na cigaba da kudu. saboda inhar na ce zan tsaya tabbas zasu kama ni. ai kuwa da gudu yayi gudu sai hajijiya ya fara kamani har azzaluman mutanen suka kusa riske ni, abun da bai wuce taku goma su kama ni ba sai na zo tsallaka titi ai kuwa ina zuwa zan zallaka sai naji wani abu ya bige ni. daga nan kuma ban kara sanin inda nake ba sai kashe gari bayan na farfado na ganni akan gadon asibiti. Ashe dai Asmeer ne ya bige ni da mota. bayan na dawo hayyacina sai na ga an daddaure raunukan da na ji. sai na yunkura zan tashi amma na gagara a dole na koma na kwanta. Asmeer da ke bakin gadona sai yake cemin sann sannan yana ce min ki hakuri ki kwanta saboda baza ki iya tashi ba bisa raunukan da ke jikin ki. ni dai ido kawai na zuba masa ina gyada kai saboda ba ni da bakin da zan iya masa magana. shi kuwa bai yi tunanin bani da lafiya ba shi dai a tunaninsa kawai duk zafin ciwo ne ya sanya ni na gagara magana. bayan wasu lokuta sai ga likita ya shigo cikin dakin da nake kwance sai ya zo yayi wasu duba dubansa a cikina sannan ya yi wasu rubutu a cikin wani takarda wanda yake kan durowa a gefena. sannan ya rubuta wasu magunguna a cikin wata takarda ya mikawa Asmeer ya ce wadannan su ne magun gunan da za a siyo. babu wata gardama Asmeer ya karbi takardar ya karanta sunan magun gunan. shi kuwa likita bayan ya mikawa Asmeer takardar sai ya fita yana cewa Allah ya ban lafiya. fitar sa ke da wuya sai Asmeer shima ya fita yana fadin Allah kara min lafiya. sai na gyada kai Alamar Ameen. sannan ya dube ni ya ce zan je na siyo magungunan da likita ya umarce ni na shiyo. da yake ba ni da bakin yi masa magana sai nayi murmushi sannan ya gyada kai. Asmeer kuwa sai ya fita yana fadin Allah kara min lafiya. Haka dai na cigaba da zama ina jinyar jikina Asmeer yana dawainiya a kaina, ya kan yawa min magana amma ni sam bana amsawa saboda bana iya magana har dai ya daina min magana saboda tsammaninsa bana son yawan magana shi yasa ya daina min magana saboda bana miyar masa maganar da yake min. Na kanyi ta kuka idan Asmeer baya nan saboda ba ni da bakin da zan yi masa godiya bisa kulawar da yake ban. haka dai na kasance cikin jinyar jikina har na kai sati biyu. ni kuwa kullum bana rabuwa da addu'o'i da kuma ibadu akan Allah ya ban lafiya game da rashin lafiyar da nake. bayan sati daya ne likita ya lura akan bana iya magana. ranan ya shigo cikin dakin da nake kwance yake ce min ya lura bana iya magana don haka zai duba min mike da muna girgiza kai kawai nayi ina murmushi alamar dai na gode. haka yayi ta dube dubensa irin na likitoti har ya gano cewa rashin maganata ba na cuta ba ce ta asiri ce. haka ya taimaka min ya kirawo wani babban malami ya min addu'o'i sannan ya ban magun gunan da zan ringa sha tare da addu'o'i da zan ringa yi. cikin ikon Allah kuwa bayan kwana biyu bakina ya bude na fara magana. Nayi murna sosai da na ji bakina ya bude wanda ya rufe tun shekaru 8 da suka wuce. kai sai da na gagara yiwa likita goodiya tsabar taimaka min da yayi. shi kuwa Asmeer bai san anyi haka ba. shima kuma likita bai gaya masa ba saboda yayi haka ne saboda Allah. To haka dai na cigaba da jinyar raunukan da ke jikina har na samu lafiya. kullum burina naga na warke na samu gagarumar kyautar da zan yiwa likita da Asmeer amma idan na tuna bani da abun da zan musu sai takaici ya lullube ni. Ranar na Asmeer yazo da wata budurwa ina kwance na juya bayana. sai na ji wannan budurwar ta ce ba baabata ba ce. ina jin muryarki sai na jiyo jiyowar da zan yi sai naga ta fita. amma da yake ba ni da ikon da zan ce ke 'yata ce saboda banga fuskarki ba. sai kawai na danne a raina ban fadawa Asmeer komai ba. amma dai jikina ya ban ke ce. kullum ina son naga kin kara dawowa Amma shiru ban ga kin kara dawowa ba har aka sallame ni na samu lafiya Asmeer ya dakko ni ya kawo ni na yiwa mahaifiyarsa godiya bisa dawainiyar da danta yake min da kuma abubuwan da take kawo min. tun muna bakin asibitin Asmeer yake son ya ji labarina amma na ce ya bari sai mun zauna zan gaya masa. to shine yanzu bayan mun gaisa da hajiya da yi mata godiya sai na budi baki zan bawa Asmeer da mahaifiyarsa labarina da naki sai kuma na jiyo sautin muryarki kin nufo gare ni. Koda fatima ta gama jin dukkanin abubuwan da baabarta ta gaya mata sai ta rungumeta tana kuka. da kyar hajiya da Asmeer da kuma baabarta suka rarrasheta ta daina kuka suna ce mata wannan ai godiya ya kamata kiyiwa Allah ba kuka ba. haka fatima ta share hawayenta. sannan ta dubi hajiya ta kwashe dukkanin abubuwan da suka faru a gareta har ya zuwa yanzu da suke zaune. baabar fatima tayi bakin ciki kwarai da gaske ai kuwa sai ta fara la'antar wadannan azzaluman mutane tare da cewa Allah ya tona asirin duk wanda ya saka su mummunar aiki na kashe hajiya da danta. gabaki daya suka amsa da Ameen. Asmeer da hajiya kuwa murna suka yi sosai game da ganin baabar fatima a gidansu. dan haka sai suka kasance da fatima da baabarta cikin jin dadi da walwala. ai kuwa nan da nan bayan komai ya dawo normal baabar fatima tayi fresh bisa jin dadin da take yi da kuma ta kulawa da hajiya take bata sai ya zamana sun shaku sosai tamkar 'yan uwan juna. suma Asmeer da fatima soyayyarsu ta kafu sosai tamkar wadanda suka dauki shekaru masu yawa suna tare domin kuwa duk inda ka ga Asmeer sai ka ga fatima. har jama.a suke cewa anya wannan ba matar Asmeer ba ce? wasu kuma su ce kodai kanwarsa ce? haka dai suka kasance tare har maganar aka yi maganar aure a tsakaninsu. babu wani bata lokaci baabar fatima ta bawa Asmeer fatima har aka yanke ranar aurensu. [8:09AM, 6/9/2015] Asmeer: *** *** *** Bakin arne da mai gidansa tare da yaran bakin arne kuwa tuni sun gama shiryawa tsaf na kashe Asmeer da mahaifiyarsa hajiya da kuma kamowa Fatima don su kawowa mai gidansu. Koda labarin dawowar baabar fatima ya riski mai gidan su bakin arne tare da saka ranar aure fatima da Asmeer cikin kankanin lokaci sai hankalinsa yayi bala'in tashi. gashi kuma Asmeer da fatima sun daina zuwa filin jirgi don koyawa fatima mota. don haka sai kawai ya ringa zuwa gidan hajiya akai akai don ya jin yanda fatima da Asmeer za su je su don ya samu damar da zai umarci bakin arne da yaransa su aikata abun da suka tsara a baya. Ai kuwa sai ya ji cewa Asmeer da fatima za su je su super market siyowa wasu kayayyake daga cikin kayan aurensu, sannan za su bi ta bayan gari don zagaya gari. sai farin ciki ya kama mai gidan su bakin arne don haka cikin gaggawa ya koma gidansa ya je ya samu bakin arne shi da yaransa ya ce maza ku shirya yanzu ku je ku tari Asmeer da fatima a can bayan gari kuyi dukkanin abubuwan da na ce. amma kai bakin arne gidan hajiya zaka tafi kai tsaye kayi dukkanin abubuwan da na tsara maka sannan ka tafo da hajiya tare da baabar fatima zuwa nan gidana don na aikata abun da nayi niyya sannan na mallaki dukkanin dukiyoyi da kadarorin da mijin hajiya ya mutu ya barwa hajiya da danta. Ai kuwa cikin cika umarni bakin arne suka fita, bakin arne ya je ya dauki mota daga jikin motocin mai gidansa, su kuma yaran bakin arne suka je suka shiga motar da mai gidansu ya siya musu don wannan aikin. sai bakin arne ya nufin gidan hajiya cikin badda kama sannan suma yaran bakin arne suka doshi bayan gari don cika umarnin mai gidan su. Dukkanin abubuwan da mai gidan su bakin arne ya tsara haka kuwa ya afku. Ai kuwa cikin sa'a daya sai ga bakin arne ya shigo da hajiya da baabar fatima cikin gidan mai gidansa duk ya daure hannayensu sannan ya rufe dukkanin bakinsu da fuskarsu da bakin kyalle sannan kuma yana rike da bindiga a hannunsa sai ya shigo da su a lokacin kuwa mai gidan bakin arne yana zaune a kan kujera a cikin falo yana jirana dawowar su bakin arne. ai kuwa yana ganin bakin arne da su hajiya sai ya cika da farin ciki, cikin murmushi yayiwa bakin arne da nuni da dan yatsansa akan ya kai su ciki, cikin bin umarni kuwa ya shiga da su. sai kawai ya je ya bude wani daki na dabam cikin gidan ya tura hajiya da baabar fatima a ciki amma kafin ya tura su ciki sai da ya bude musu dukkanin fuskokinsu. bayan ya saka su a cikin dakin sai ya turo kofa ya rufe. hajiya da baabar fatima kuwa sai kuka suke suna cewa ina ka kawo mu ne kai waye? amma bakin arne ko kula su bai yi ba. sai kawai ya ja kofa ya rufe. Ashe ita baabar fatima ta gane bakin arne domin kuwa shine ogan azzaluman mutanen nan da suka kamata a can kauyen da take da zama. amma sai tayi shiru ba ta gayawa hajiya ba saboda kar hankalinta ya kara tashi. sai kawai ta taya hajiya kuka tare da salati suna neman taimako daga Allah. shi kuwa bakin arne bayan ya tura su hajiya cikin dakin sai ya dawo wajen mai gidansa suka zauna suna jiran zuwa yaran bakin arne da Asmeer da fatima. Suma yaran bakin arne abubuwan da mai gidansu ya tsara musu haka suka bi, sai sai kuma kash! a wajen da suka samu matsala shine lokacin da suke harbe "yan sandan da su tare da su Asmeer. da yake Asmeer da fatima ba su fita a motar ba "yan sanda ne kawai suka bude kofar motar suka fita don yiwa yaran bakin arne wadanda suka yi shigar maroka magana. da fitar su kuwa yaran bakin arne suka bude musu wuta suka harbe su. Ai kuwa Asmeer yana jin karar harbi an harbe "yan sandan da suke tare da su cikin dimaucewa ya danna ribas ta baya har sai da ya taka gawarwakin "yan sanda. babu wata wata ya cigaba da ribas cikin hanzari babu kakkautawa don ya tsiratar da ransa shi da fatima. da yake yaran bakin arne da motar su zo wajen, sun fakata a can wani bangare na daban cikin hanzari suka je suka shiga motar suka bi su Asmeer. Asmeer da ya lura mutanen nan sun biyo su da mota sai ya kara karbin ribas. amma duk da haka sai da wadannan mutanen suka kusan riskarsa duk da tazarar da ya basu a lokacin da ya iyo ribas din saboda mutar mutanen zata fi gudu fiye da ta su Asmeer. Da Asmeer ya ga mutanen sun kusa cimma sai ya dan rage gudu sannan ya juya motar da nufin juyata daga ribas din da yake yi. ai kuwa yana juya ta sai ya ji motar ta mutu bisa rashin mai. domin kuwa tun suna super market Asmeer ya lura babu mai a motar amma ya bari idan ya je gidan mai wanda yake can bayan gari sai ya sha. koda Asmeer ya ji motar ta mutu sakamakon babu mai. sai ya fita a motar sannan ya umarci da fatima su gudu su shiga jejin da yake tsalleke da titin amma sai fatima ta ce kazo mu bi titi mana watakil mu samu wanda zai taimaka mana cikin daka tsawa ya ce ya za mu bi titi kai tsaye ai idan mun bi titin za su ji dadin kama mu. ai kuwa suna cikin haka sai Asmeer ya hangi wadannan mutanen da suke binsu sun kusan karisowa. cikin hanzari Asmeer ya finciki hannun fatima ya ja ta da gudu suka lallaka cikin jejin da yake gefe da titin. haka suka nausa ciki suna gudu. su kuwa wadannan mutanen da suka kariso wajen motar su Asmeer sai suka faka a gefe domin kuwa tun daga nesa sun hangi Asmeer da fatima sun fita a motar sun shiga cikin jeji. ai kuwa suna karisowa wajen motar su Asmeer sai dukkaninsu suka fice a motarsu suka bi bayan Asmeer da FATIMA ZAHRA.FATIMA ZAHRA.../ RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 27 RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 27 Posted by Bashir Sani Fesan on 28 Dec 2016 - 13:53 Asmeer da fatima gudu suka cigaba da yi a cikin jejin babu kakkauta. su ma kuwa yaran bakin arne cigaba da bin Asmeer da fatima suka cigaba da yi. suna rike da bindigogi. da yake su Asmeer sun basu tazara sosai sai daya daga cikin yaran bakin arne ya daga murya ya ce ku dakata idan ba haka ba kuwa za mu harbe ku. Asmeer da fatima kuwa gudu suka cigaba da yi basu tsaya ba. haka dai yaron bakin arnen ya cigaba da cewa inhar baku tsaya ba fa za mu harbe ku. gudu da yayi gudu sai fatima da fara haki tana cewa brother na ga ji fa. sai Asmeer ya ce ki daure dai nasan baza a rasa wani dan karamin kauye a nan gaban mu ba. haka dai ta daure suka cigaba da gudu sai dai kuma Asmeer ya wuce ta saboda fatima ta ga ji sosai saboda gudun da suke yi, sai Asmeer yake ce mata ga su can fa suna kokarin kama mu ki kara gudu fa. ita kuwa fatima sai haki take yi. koda gudun ya yiwa fatima yawa sai kawai ta daina gudu tana sassarfa sannan tana haki tamkar kirjinta zai tsage. muryarta a shake take cewa Asmeer wallahi na ga zuciya ta zata fito. sai Asmeer shima ya rage gudu yana haki yana cewa kanwata ki kara daurewa dai idan sun kama mu fa kashe mu za suyi saboda sun harbe "yan sandan da suke kula da mu. dan haka ki hakuri ki kara gudu mu dan kara gaba ko Allah zai sa mu riski kauye a gaban mu. Da kyar fatima da dan kara gudu koda ta yi dan kara min gudu sai kawai jiri ya debeta ta fadi kas tana haki tana cewa wayyo Allah na zan mutu. Asmeer yana ganin fatima ta fadi sai ya tsaya sannan ya durkusa a gabanta yana haki yana cewa ki daure ki tashi mu gudu ga su can fa sun tun ka ro mu. fatima tana daga kwance cikin shashshakar murya tare da nishi ta ce brother na wallahi bazan iya cigaba da gudu ba kirjina yana bugawa tamkar zai tsage sai kawai ta fashe da kuka ta ce brother na ka gudu ka tseratar da ranka, ka bar ni su zo su kashe ni, kai dai ka gudu ka tseratar da ranka, ni dai tawa ta zo karshe, sai kawai ta kara fashewaa da kuka Babu zato babu tsammani sai hawaye suka kwararo daga idanuwan Asmeer ya ce haba! mi yasa ki ke cewa haka. bazan iya guduwa na barki a nan ba balantana har su zo su riske ki a nan. Su kuwa masu bin su Asmeer koda suka ga fatima ta fadi a kas sannan Asmeer ya tsaya sai suka cika da murna suna cewa yauwa ga su can sun tsaya maza mu kara gudu muje mu kama su, ai kuwa sai suka kara kaimin gudunsu. Asmeer yana daga durkushe a gaban fatima yana cewa ta tashi su gudu sai kawai ya hango mutanen da suke binsu sun kusa cimma musu, a kidimauce Asmeer ya kama hannayen fatima ya tayar da ita sannan ya kamo kugunta sannan ya dora hannunta na dama ya dora a kafadarsa sannan ya ja ta da kyar ya tallafa mata suka tafi. Da yake sun zo daf da wata duhuwa sai kawai Asmeer ya ja fatima suka shiga cikin duhuwar jejin. Mutanen da ke biye da su kuwa koda suka zo daf da wajen duhuwar da su Asmeer suka shiga sai suka tsaya cak suna dariyar mugunta suna cewa ai gudunsu ya kare. sai daya daga cikin yaran bakin arne ya ce mutum biyu su shiga ciki su duba su sannan su fito da su. mu kuma za mu tsaya a nan idan munga sun fito sai mu kama su. hakan kuwa aka yi sai mutane biyu suka shiga ciki suna duba su. Abu kamar wasa sai suka nemi su Asmeer sama da kasa suka rasa, har suka fara gajiya da nemansu wadanda suke wajen duhuwar sai suma suka shigo ciki su ka cigaba da neman su Asmeer amma shiru ka ke ji " wai malam ya ci shirwa." sai da suka doke rabin sa'a suna neman su Asmeer amma ba su same su ba har suka fara shawartawa su koma kawai. Asmeer da fatima kuwa suna can ciki sun shiga cikin wani sarkakiya ida babu wanda zai iya ganinsu saboda duhun wajen. da yake fatima tana nishi sosai sai Asmeer ya ce ta rufe bakinta kar su jiyo sautin numfashinta haka fatima da rufe bakinta sannan ta sassauta jan numfashinta. suna wajen suna la6e sai suka jiyo muryar mutanen suna cewa mu tafi kawai don baza mu samu su ba. da ya ke mutanen sun rarrabu ne sannan kuma akwai daya daga cikin su wanda yake kusa da su Asmeer amma baya ganinsu saboda suna cikin duhu sai kawai ya juya zai tafi ya bar wajen. Su Asmeer kuwa suna ganin duk zirga zirgan da suke yi. to da wannan wanda yake kusa da su ya juya zai tafi sai fatima ta yi arba da mummunar fuskarsa bata san lokacin da ta bude baki za tayi kara ba. cikin zafin nama Asmeer ya yi farat ya rufe mata baki. amma duk da haka sai da sautin karar ya fito. ai kuwa sai wannan wanda yake kusa da su Asmeer sai ya juyo da sauri ya nufi wajen da sautin karar ya fito ai kuwa yana zuwa daf da wajen sai ya ga karangiya talullube wajen sai kawai ya yaye karangiyar. ai kuwa yana yayewa sai ga Asmeer da fatima a tsaye a wajen suna muzurai da idanuwansu. fatima jikinta sai rawa yake yi. [9:12AM, 6/12/2015] Asmeer: Sai kawai yayi kuruwa ya budi baki ya ce ku zo ku ga....kafin ya karisa sai Asmeer ya dunkule hannunsa ya zabga masa naushi a fuska, sai jini yayi tsurtuwa daga fuskarsa nan da nan kuwa ya cilla wani ihu sannan ya fadi kasa sumamme. su kuwa sauran yaran bakin arne ashe sun ji kuruwar da daya daga cikinsu yayi ai kuwa sai suka nufo wajen da suka ji ihun daya daga cikin su. Asmeer kuwa bayan ya naushi wannan mutumin sai ya kama hannun fatima ya ja ta suka bar wajen da gudu amma ina gudunsu duk a banza domin kuwa tuni wadannan mutanen sun riske su sai kawai daya daga cikin mutanen ya yi nuni da bindigarsu a Asmeer ya ce ku dakata ko na harbe ku. koda Asmeer ya ga anyi terget nasu da bindiga sai Asmeer da fatima suka tsaya cak. sai su ma wadannan mutanen suka tsaya sannan suka kewaye su Asmeer. sai daya daga cikinsu ya fashe da dariya ya ce kun gama gudunku mun kama ku dan haka ku wuce mu fita daga cikin duhuwar nan sannan mu aikata abun da aka umarce mu mu aikata. sai Asmeer yayi musu wani irin kallo na reni sannan ya fara wani irin huci tamkar zaki a cikin dawa. suna jin hucin da Asmeer ya ke yi sai suka razana ainin suka fara kallon kallon a Asmeer. sai daya daga cikin su ya biyo ta bayan Asmeer da nufin ingizashi su tafi. ai kuwa yana taba Asmeer. cikin zafin nama Asmeer yayi wani kuruwa ya sure shi ya makashi da kasa sai jini ya fara malala daga hancinsa da bakin sai shima nan take ya suma. sauran mutanen suna ganin haka sai suka tsoruta da Al"amarin Asmeer sai suka ce a ransu anya wannan mutum ne? sai suka fara ja da baya. su har sun manta suna rike da bindigogi. sai daya daga cikin su ya kalli Asmeer ya kai ka wuce mu tafi cikin salama idan ba haka ba kumamu harbeka a nan. sai Asmeer ya kalli wanda yayi managar ya ce da shi ku su waye? sannan waye ya aiko ku ku kashe mu? sai daya daga cikinsu ya ce mai gidan mu ne ya umarce mu mu zo mu aikata kisa a gare ka sannan mu tafi da wannan budurwar wacce kake tare da ita dan haka ka wuce mu tafi. suna cikin haka sai daya daga cikinsu ya lallabo ta bayan Asmeer ya biga masa kasin bindiga. buga masa da yayi ne ya sanya Asmeer ya fadi kas sumamme. ita kuwa fatima sai ta calla wani uban ihu ta ce wayyo sun kashe min dan uwana masoyina sai kawai ta durkusa a gaban Asmeer tana kuka. su kuwa mutanen sai suka kece da dariyar mugunta sannan daya daga cikin su ya umarci daya daga cikinsu ya dauki Asmeer su fita da shi daga cikin duhuwar jejin. cikin cika umarni kuwa suka ture fatima suka cincibi Asmeer suka fita da shi sannan suka angiza fatima wacce take ta rusa kuka suka fita da ita daga duhuwar jejin. Bayan sun fito ne sai daya daga cikin su ya dakko waya daga aljihunsa ya kira mai gidansu sai ya ce ranka dade ga su nan a hannun mu fa mun kama su har mun sumar da Asmeer saura mu kashe shi kawai. sai mai gidan ya ce ina fatan bai mutu ba sai ya ce eh ranka dade bai mutu ba sai ya ce mu su yauwa to kar ku kashe shi ina son na kashe shi da hannuna saboda kafin ya mutu akwai abubuwan da nake so na ce masa dan haka ku kwatanta min dai dai wajen da kuke sai na zo ni. sai ya kwanta masa wajen sannan ya ce idan kazo zaka ga motarmu da tasu a gefen titi to sai ka tsallo ka shi domin kuwa sun gudu ne kafin mu kama su. sai mai gidan nasu ya ce to gamu nan muna zuwa da bakin arne. sai ya ce ranka dade sai kun zo. Abun da bai wuce rabin sa"a ba sai suka iso wajen shi da bakin arne. fatima tana zaune a kusan Asmeer da yake a lokacin Asmeer ya dawo daga dogon suman yake. Asmeer yana ganin ganin wannan mutumin wanda ya saka wadannan mutanen don su kashe Asmeer Ashe shine manajan babban kamfanin mahaifiyarsa. Asmeer da fatima suna ganinsa sai suka mike cikin murna suna cewa yauwa manaja kwanda da kazo sai suka je suka tsaya a bayansa suna cewa ka taimaka mana za su kashe mu. Manajan yana jin haka sai ya kece da dariyar mugunta sannan ya jawo Asmeer daga bayansa ya kwashe shi da mari ya ce waye zai taimake ka? Ai ni nasa A kashe ka sannan a tafo min da fatima don na aureta, yanzu haka uwarka da baabar fatima suna hanuna zan kashe uwarka wato hajiya ita kuma baabar fatima da yake sirukata ce bazan kashe ta ba. sannan yanzu haka dukkanin kadarorin da mahaifinku da ya bar maka suna hanuna kudaden da suke cikin bank na kune kawai ba su zo hanuna ba saboda da sign naka ake fitar da kudade daga bank dan haka shine nazo wajenka kasa min hannu don na mallaki tarin dukiyar da ke cikin bank na ku.... kash! mu hadu a part 28 don jin cigaban labarin.uka nufi hanyar gida. ba tare ya je yayiwa matar sallama ba. [1:23PM, 5/31/2015] Asmeer: Bayan sun dawo gida sai Asmeer yake tambayar fatima dalilin da yasa take kuka? sai fatima ta ce masa wannan matar da muka je wajenta ba ita ba ce baabata saboda ita baabata bata magana. sai Asmeer yace mata eh gaskiya wannan matar kuwa tana magana. domin kuwa tun lokacin da aka gama mata aiki a asibiti da ta dawo hayyacinta na ji tayi magana. sai fatima ta ce to ka ga kuwa ba baabata ba ce. sai Asmeer ya ce to ai da kin tsaya kun gaisa kika sani ko ita ce Allah ya bata lafiya ta fara magana. sai fatima ta ce hmmm..baabarta wa da anyi mata magani har an ga ji. sai Asmeer ya ce to ai Allah mai iko ne akan komi nasa. dan haka ki daure mu koma ku gaisa. sai fatima ta ce a"a bazan koma ba. haka dai Asmeer ya dage lallai ta je ta gano ko ita ce. Amma sam fatima taki yarda. a dole ya hakura. shi kadai yake zuwa wajen wannan matar ya mata hidima ba tare da fatima ta je ta ba. ita kuwa fatima ta kasance cikin halin damuwa na rashi baabarta domin kuwa ko a talabijin ko gidan redio ko a jarida bata ji ana cikiyarta baabarta ba. sai ya zamana ta kasance cikin damuwa da tunanin baabarta. hajiya kuwa kullum tana rarrashinta tana bata hakuri kan cewa inhar baabarta tana raye babu shakka wataran za su hadu. hakan ya san fatima ta rage damuwa. Kamar duk wata yanda hajiya ta saba zama a can wani kawataccen gidan don biyan ma"aikatanta yau ma haka ne sai dai kuma wannan watan a gidanta akayi taron saboda wasu dalilai nata. Bayan an gama fitar da dukkanin ribar da aka samu a wannan watan sannan ta ware kudaden da ake biyan ma"aikatanta na gida da na sauran kamfanoninta. Bayan ta sallamin kowa sai ta dakatar da babban manajanta ta ce masa ya dakata akwai maganar da take so suyi. Bayan manajan ya zauna sai hajiya ta dube shi ta ce masa yauwa manaja na daman kamar yanda na maka alkawari zan biya maka kudin saudiya kamar yanda na saba duk shekara to wannan shekarar ma zan biya maka kai da yayarka. sannan na kara maka albashi akan na da, ina biyanka naira million biyu duk wata to yanzu zan ringa biyanka naira million biyar na kara maka million uku ke nan. baya ga haka akwai sabon gidan da na gama ginawa a nan kusa da mu to na bawa yayyarka. koda manaja ya ji irin kyaututtukan da hajiya ta mishi sai yayi godiya kwarai da gaske har da zubar da hawaye. sai hajiya ta ce haba! manaja ai wannan ba abun kuka ba ne ka cancanci na maka dukkanin wadannan abubuwan bisa rike dukiyar mijina amana da kake yi tun yana raye har ya zuwa yanzu. sai manaja ya ce dole nayi kuka ai bisa wannan alkairi da kika min babu abun da zan ce miki sai dai na ce Allah ya saka da alkairi ya kara bunkasa kasuwancinki ya kuma kare ki daga dukkanin mahassadanki. Sai hajiya tayi murmushi sannan ta ce Ameen. sai hajiya ta ce sai dai kuma har yanzu ba ka kara aure ba tun rasuwar matarka tafarko baka kara aure ba. sai ya sukuyar da kansa cikin kunya ya ce eh ina shirye shirye. amma zanyi insha"allah. sai hajiya ta ce ko dai kana so na nema maka wata bazawara ce? sai ya saka dariya ya ce haba! hajiya ki bari kawai zan nema da kaina na fi son na auri budurwa saboda yanzu an daina yayin bazawara. sai hajiya ta saka dariya ta ce an daina yayinmu, sai ya ce a"a ai ba ke nake nufi ba. sai ta ce har nima mana tunda nima ina jerinsu, to bari ka ji bazawarorin sun fi akan "yan mata. sai manaja ya sa dariya ya ce hajiya ke nan. sai ta ce hajiya ko gaskiya. sai manaja ya sunkuyar da kansa yana murmushi tsabar kunya. sai ya ce to hajiya ni kam zan tafi. sai ya mike da nufin tafiya sai hajiya ta ce af ban gaya maka abun da ya faru da ni da dana ba da kuma fatima. sai manaja ya dawo ya zauna ya ce mi ya faru da ku?sai hajiya ta nisanta ta ce nasan baka san abubuwan da suka faru da ni ba da kuma abun da aka shirya mana ni da dana Asmeer na kashe mu da aka yi niyar yi. saboda kai a lokacin ka ce min ka tafi kwatano duba kayayyakina na can. A fusace ya ce kashe ki kuma hajiya ke da danki da fatima wacce kike son ta zama sirukarki? sai hajiya ta ce eh. sai ya ce mi ya faru haka? sai ta kwashe dukkanin abubuwan da ya faru da zayyana masa. ai kuwa yana ji sai kawai..ANKO BOOKS [8:43AM, 6/2/2015] Asmeer: <<>>Part 24. ...Ai kuwa yana ji sai kawai ya ce hajiya abubuwan da suka faru da ke ke nan, to amma an gano wanda ya saka a aikata hakan kuwa? sai hajiya ta ce A"a ba a gano ko waye ba amma police suna bincike. sai manaja ya ce tabbas mahassadanki ne suke kokarin ganin bayanki don su ga sun mallake dukiyar da kika tara, yanzu abun da yafi shine zan samu miki masu tsaronki suna kula da lafiyarki. sai hajiya ta ce ai an kawo min police guda biyar masu kula da lafiyata da na dana da fatima. sai manaja ya ce to amma ya akai ban gansu ba? sai hajiya tayi murmushi ta ce akwai guda daya biyu a waje sauran kuma sun raka su fatima da Asmeer super market. sai manaja ya numfasa ya ce kwarai kuwa da zan shigo na ga police guda biyu sai da suka caje ni tukun na shigo nan. sai hajiya ta ce ai mutanan da suke kokarin ganin bayana insha"allah ni zan fara ganin bayan su domin kuwa akwai wani shiri da nake yi akan su yanda zanyi saurin gano su. a firgice manaja ya ce wani irin shiri kike yi akan su hajiya? ganin yanda manaja ya firgita ya bawa hajiya mamaki sai ta dubi manaja ta ce ya naga ka firgita haka? lafiya kuwa? cikin sunkuyar da kansa ya ce a"a babu komai kawai jin cewa akwai shirin da kike yi ne akan mutanan nan ne abun ya ban mamaki saboda kina mace har akwai abun da za kiyi alhalin ga mu nan muna nan mu ya kamata mu dauki matakin ganin bayan azzaluman mutanen nan. sai hajiya tayi murmushi ta ce haba! manaja na kasan na yarda da kai sosai dan haka ba zan iya 6uye maka komai ba game da abun da yake faruwa a gare ni. sai manaja ya murmusa ya ce haka ne hajiya. sai hajiya ta dago da kanta ta ce kasan dana yana daf da auren fatima sannan ya daina shaye shaye ya nutsu don haka yana yin auren zan mika masa komai na kasuwancin mahaifinsa shi zai ringa juyawa sannan shi zai ringa biyan ma"aikata albashi da dai sauran kulawa da dukkanin dan kasuwa yake bawa kasuwancinsa. sannan daman ba wani abu nake shiryawa wadanan mutanen ba illah... kafin ta cigaba sai ta ji sallamar Asmeer da fatima sun shigo. cikin murmushi hajiya ta dauke hankalinta daga kan manaja ta kalli fatima da Asmeer ta ce sannunku da dawowa "ya "yana. sai dukkaninsu suka ce yauwa hajiya. wani irin kallo Asmeer yayiwa manajan hajiya, koda manaja ya ga irin kallon da Asmeer ya saba yi masa cikin sauri ya sunkuyar da kansa da yake daman Asmeer ya saba yi masa irin wannan kallon mai dauke da Allah wadaran. Domin kuwa Asmeer yasan munanan halayen manaja wanda hajiya bata sansu da shi ba domin kuwa manaja ya saba zuwa gidan karuwai ya debowa karuwai yana lalata da su a gidansa, sannan kuma Asmeer ya sha ganin manaja a gidan giya da wajen caca. amma manaja bai taba ganin Asmeer a irin wannan guraren ba sai lokacin da wata karuwa ta zo wajen Asmeer yana zaune a wajen da yake shan giyarsa sai karuwar ta zo ta zauna kusa da Asmeer take ce masa ranka ya dade tun ba yau ba nake son yi maka magana ina tsoro sai yau domin kuwa na dade ina sonka. sai Asmeer ya daka mata harara ya ce ke ni duk iskancina ba na bin matan banza. sai wannan karuwar ta ce eh na ji amma ka yarda da ni ko sau daya. A fusace Asmeer ya mike ya kalleta ya ce mata na ce miki ni bana hulda da matan banza ki hanzarda barin nan wajen ko na wulakantaki. sai wannan karuwar tayi masa wani irin kallo mai dauke da ka tausaya min. sai ta rike rigarsa tana cewa ka taimaka min kazo muje jost sau daya ne fa. cikin 6acin rai Asmeer ya mike tsaye ya dauki hannunsa ya gaura mata mari ji kake tassss...sai da kowa wanda yake wajen ya kallo wajen to a lokacin kuwa manaja yana zaune a ta bayan Asmeer bai san Asmeer ba ne sannan kuma karuwar da ya mara yarinyar manaja ce don haka a fusace manaja ya taso ya rike rigar Asmeer ta baya sannan ya dauki hannu zai kaura masa mari. ai kuwa manaja yana arba da fuskar Asmeer sai ya saki rigar Asmeer take a wajen jikinsa ya fara karkarwa. shi kuwa Asmeer yana ganin manaja ne ya rike rigarsa ta baya har yana kokarin marinsa sai kawai ya kalli manajan kasa da sama bai ce masa komai ba sai kawai ya fice a bar wajen. ita karuwar da ta ga Asmeer ya fice ya bar wajen. ita kuwa karuwar sai take cewa manaja pls ka taimaka min ka je ka dawo min da waccan guy din ina son shi wallahi. manaja a fusata yayi agame da abun karuwar ta ce sai kawai ya gaura mata mari ya ce baki da hankali ne kin san ko shi waye? hada rai tayi ta ce oho ko shi waye ina son shi. ran manaja kara baci yayi sai kawai ya daka mata tsawa ya ce kin cuceni kika saka na zo na kusa na marin dan uwar gidana. sai kawai karuwar ta ce malam daina min tsawa. ina ruwana ko shi waye a wajenka. sai kawai manaja ya fita a wajen bai kara dawowa wajen ba. To shine tun daga ranar bai kara dawowa wajen ba sannan yake jin kunyar Asmeer sosai. shi kuwa Asmeer babu abun da yake cewa manaja sai harara kawai. ko sako hajiya ta bawa Asmeer ya kaiwa manaja sai dai kawai ya kai masa babu wata magana da take shiga tsakaninsu. sai ya zamana manaja yana tsoron Asmeer sosai. sai dai abun da yayiwa manaja dadi shine abun da ya faru a tsakaninsu bai gayawa hajiya ba. da ya gayawa hajiya tabbas da yaga canjin fusaka a wajen hajiya. [9:43AM, 6/3/2015] Asmeer: wannan shine dalilin da yasa duk lokacin da Asmeer ya kalli manaja sai ya daka masa harara. shi kuma manaja sai ya sunkuyar da kansa. ita kuwa hajiya bata taba lura da abun da yake gudana a tsakanin Asmeer da manaja ba. Bayan Asmeer ya wuce ya shiga daki. ita kuma fatima zata wuce sai da ta durkusa ta gaida manaja don girmamawa. Manaja kamewa yayi da ya ji irin sautin muryarta. domin kuwa sai yanzu ne ya saurari sautin fatima mai rikirkita kunnuwa, bai taba miyar da hankali ya saurari sautin muryar fatima ba sai wannan karon, ai kuwa sai ya ji kirjinsa ya buga da karfi. Hajiya ce ta masa magana sannan ya dawo hayyacinsa. sai hajiya ta dube shi ta ce babban manajana lafiya kuwa naga ka kidimauce haka? kikinar dole ya fara yana cewa aaaa"aaaa babuuuu komai hhhhajjjjiya. sai hajiya ta yi murmushi ta ce ka fada mana akwai abun da ke damunka. mikewa yayi daga kan kujera ya ce ni kam zan tafi hajiya na gode sosai da alkairan da kika min. sai hajiya ta tashi ita ma tana cewa babu komai babban manajana ai komi na maka ka dace a maka hakan. har manaja ya fita a falon gidan godiya ya ke yi. haka dai ya fita ya je ya shiga mota ya bar gidan. *** *** *** Batun matar da Asmeer yake kula da ita a asibiti kuwa haka Asmeer ya cigaba da bata kulawa har ta samu lafiya. bayan ta samu lafiya sai aka sallameta sai Asmeer yake tambayarta yanzu ya za ayi game da komawarki gidanku? sai matar take cewa ita bata da kowa a garin nan, sai dai kuma akwai wani kauye gabas da garin nan wanda a akwai gidan wata mata wacce nake zama a gidanta. sai Asmeer yake cewa to ko kin san sunan kauyen sai ta ce eh na ji dai ana cewa kauyen katsinawa. sai Asmeer ya ce au anan kauyen kike? kinga kuwa kwanan nan mukayi wani kes a chan. ashe a nan kauyen kike? sai ta ce eh amma kuma ina tsoron komawa saboda akwai wasu azzaluman mutane da za su iya su kamani. abun da matar ta fada ya bawa Asmeer mamaki sai dubi matar ya ce wasu mutane ne haka? sai matar ta ce eh ai kasan tun da ka kawo ni wannan asibitin ban taba gaya maka labarina ba da kuma abun da ya same ni. sai Asmeer ya ce eh haka ne. sai matar ta ce yanzu dai babu lokacin da zan baka labarina sai mun samu waje. sai Asmeer ya ce to mi zai hana mu je gidanmu na kai ki ku gaisa da mahaifiyata. sai matar ta ce gaskiya ne dan kuwa ina so na ce maka ka kaini wajen mahaifiyarka na mata godiya bisa kyautatawar da take nuna min. sai Asmeer yayi murmushi ya ce ai mahaifiyata tana tausayin duk mutumin da yake cikin wani hali na tausayawa. sai matar ta ce Allah sarki gaskiya yi sa"ar mahaifiya. sai Asmeer ya sau murmushi sannan ya ce sai ki zo muje mu shiga mota mu tafi. haka matar ta bi Asmeer suka je suka shiga mota suka nufi gidansu Asmeer. *** *** *** A can bangaren su bakin Arne da maigidansa kuwa cigaba suka yi da tarkon Asmeer da hajiya. sai mai gidan bakin arne ya zo ya samu bakin arne yake ce masa kai jiya fa na je gidan hajiya na jiyo wasu abubuwan da ya tayar min da hankali sannan kuma zuciyata ta tafo da son wata yarinya da ta rkirkita min zuciyata wanda inhar ban mallaketa ba zan iya shiga wani hali. baya ga haka inhar ba mu tashi mun kashe hajiya da dan taba ina daf da rasa matsayina da nake da shi a wajen hajiya domin kuwa dukkanin wasu harkokin kasuwancinta na nan Nigeria da na kasashen zata damkasu ga danta Asmeer. inhar ta damkasu ga hanunsa kuwa tawa ta zo karshe sannan kaima baza ka samu abun da na ce maka ba. dan haka dole mu hallaka hajiya da Asmerr cikin kwanaki kalilan. koda bakin arne ya ji haka sai ya mike yana huci yana cewa mai gidana a yau dole hajiya da danta har da wannan yarinyar su bakunci lahira. ta shi yayi cikin sauri ya ce baka da hankali ne za ka ce har da wannan yarinyar wato fatima wacce yanzu ta zamo min mahadar rayuwata. sannan na ji ka ce yau za a kashe hajiya da danta to ka sani akwai "yan sanda tattare da ita da Asmeer dan haka dole mu mu san hanyar da za mu bi mu kashe su ba tare da police son sani ba kuma nan da sati ya kamata mu gaba bayan su....AHRA novels / RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 25 RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 25 Posted by Bashir Sani Fesan on 28 Dec 2016 - 13:46 nan da sati ya kamata mu ga bayansu. bakin harne huci yayi tamkar ya ci babu ya ce mai gida an gama, sannan nan a yau din nan zan hada sababbin yara wadanda za muyi aikin da su, amma shin so kake a shiga har cikin gidan hajiya a kashe su ko kuwa kafi son a tare su a hanya a kashe su? Shin da bindiga kake so a harbe su ko kuwa yankan rago kake so ayi mu su? koda ya ji haka sai ya ce babu ko daya, yanzu dole mu san hanyar da za mu gama da su ba tare da wata matsala ba kuma ba tare da an san ni na kashe su ba, kuma dole nasan hanyar da zan bi na mallaki fatima ko ta yaya. sai bakin arne ya ce ai mallakar fatima mai sauki ne mai gida, kai dai ka kwantar da hanlinka tamkar ka mallaki dukkanin abun da kake so. tun tsurewa yayi da dariya sanan ya dubi bakin arne ya ce shi yasa nake son na sakaka aiki saboda baka da tsoro kuma baka da imani. sai ya saka hannunsa a aljihu ya fiddo da bonch din dubu dubu ya mika masa ya ce ga wannan ka je ka nemo wanda za kuyi aikin. koda bakin arne ya ga wannan dubin kudin a hannunsa sai ya kece da dariyar mugunta ya ce sai mai gidana tabbas duk wanda zai ma aiki dole yayi cikin gaggawa saboda kana sake hannu. sai bakin arne ya fiddo da sigari ya bunka mata wuta sannan ya zuka ya busa hayakin a saman silin falon, sannan ya juya ya fita yana cewa mai gida sai na dawo. sai ya ce yauwa ina jiran ka fa. kafin ka dawo zan san ta yanda za a kashe hajiya da danta sannan na mallaki FATIMA ZAHRA. *** *** *** Asmeer da matar da ya taimawa shigowa cikin falo suka yi tare da sallama, amma da yake babu kowa a cikin falon babu wanda ya amsa musu sallamar. bayan sun shigo sai Asmeer ya nunawa matar kujera ya ce mama ga waje ki zauna bari na je na kira momina tana ciki. cikin murmushi ta ce to dana. sai matar ta zauna. zaman da tayi ne akan kujera zai tabbatar maka bata saba zama a irin wannan kujera ba, zaman ta ke da wuya sai ta fara kalle kallen falon tana ganin irin kawatuwar da yayi da kuma irin abubun da aka saka a cikin falon, kai ka ce gidan governor ne. sai kawai matar ta rike baki ta ce 0 wannan ai ita ce aljannar duniya sai ka ce ba a duniya ba. kai Amma masu kudin suna jin dadi. uhm! Allah mai azurta wanda yaso sannan ya talautar wanda yaso cikin ikonsa da adalcinsa... Tana cikin wannan kale kalen da mamaki sai ta ji hajiya ta ce sannunki da zuwa. cikin murmushi ta ce yauwa hajiya. sai hajiya ta je ta bude firij din dake cikin falon da dakko 5alive mai sanyi sannan da dakko wani plate da kofi daga cikin firij din ta kawo gaban matar, da kanta hajiya ta bude lemon ta zuba a kofi tana cewa Ashe ke ce matar da dana ya biga da mota? sai matar ta ce eh nine wallahi. a dai dai wannan lokacin ne hajiya ta gama zuba mata lemon a kofi sannan ta ajiye a gaban matar.sai hajiya ta ce gashi ki kashe kishirwa. cikin kunya ta ce to nagode kwarai da gaske sai ta dauki kofin wanda yake dauke da lemon. sai ta sha sannan ta ajiye guntun. sai hajiya ta dubeta ta kara cewa jiki yayi karfi sai matar ce Alhamdulillah jiki ya warware. sai hajiya ta ce haka ake so. sai matar ta ce daman godiya na zo na miki bisa alkairin da kika min na aiko min da magun guna da abinci da kuma dawainiyar da danki ya min. sai hajiya ta yi murmushi ta ce Ayyah ai babu komai. shi kuwa Asmeer bayan ya je ya gayawa hajiya sai ya je ya hau matakala ya nufi dakin Fatima. koda ya je bakin dakin sai ya kwankwasa tare da kiran kanwata...ita kuwa fatima a lokacin barci ta ke yi. shi kuwa Asmeer bai gushe ba ya cigaba da kwankwasawa yana cewa kanwata kina ina ne kizo ki bude. hajiya tana daga can kasa sai ta jiyo kiran da Asmeer yake yiwa fatima sai ta ce masa barci da take yi dazun nan muna kallon news ta shiga dakin ta ce barci take ji ka barta tayi barcinta ta huta. koda Asmeer ya ji haka sai ya sakko yana fadin kash! ai na so ta zo ta gaisa da matar nan. haka ya sakko ya dawo wajen da hajiya suke zaune. a lokacin kuwa matar ta gama yiwa hajiya godiya. dan haka lokacin da Asmeer ya zo sai ya cewa matar yauwa wannan ita ce momina. sai matar ta ce ai mun gaisa. sai Asmeer ya ce ai naso ku gaisa da kanwata ma sai kuma gashi tana barci. sai matar ta ce Ayyah ai bakomai. sai Asmeer ya nisanta ya ce yauwa daman kin ce sai mun zo nan zaki ban labarinki. hajiya cewa ta yi Laaa! ka ji min dan nan ya za ka ce ta baka labarinta? sai matar da sau gutun murmushi ta ce aaa bakomai hajiya ai ni na ce zan gaya masa. sai hajiya ta ce to naga bai kamata ya ce sai ya ji labarinki. sai matar ta ce kar ki damu hajiya nima na ji dadin tambayar da ya min. sai hajiya ta ce to shi ke nan sai ki gaya masa labarinki. ita kuwa fatima tana cikin barcinta sai take mafarkin baabarta ta ringa mafarke mafarke marasa ma"ana akan baabarta. a firgice ta tashi tana salati. tana farkawa kuwa sai ta jiyo maganganu daga cikin falon. cikin sanyi jiki ta mike da je ta bude kofar dakinta a hankali don ta leka su waye da waye a falon. ai kuwa tana lekowa sai tayi arba da fuskar baabarta. [9:22AM, 6/5/2015] Asmeer: ji tayi kirjinta ya buga da karfi. sai kuma ta fara murtsuka idanuwanta tana cewa mafarki nake yi ne ko kuwa gizon baabata nake gani. da ta ga dai da gaske baabarta ce sai kawai ta bude kofar dakinta da sauri ta sakko kasi, tana kiran baaba! baaba!! baaaba!!! tsabar murta da saurin da take yi sai da ta fadi a kan matakalar, jin faduwar da tayi ne Asmeer da hajiya suka juyo da sauri, ita kuwa baabarta ta bude bakinta ke nan za ta bawa su Asmeer labarinta sai ta jiyo kiran da fatima take mata da kuma faduwar da tayi, koda ta waiga ta ga fuskar fatima sai ta mike da sauri ta je ta daga ta daga faduwar da tayi. Fatima tana ganin. baabarta ce ta dagata sai ta rungumeta tana kuka tana cewa baabata daman baki mutu ba. sai itama hawaye ya kwararo daga idanuwanta tana cewa ban mutu ba "yata. Asmeer da hajiya kuwa tashi suka yi daga kan kujera suka tsaya suna mamakin su fatima da baabarta, ganin yanda suke zubar da hawaye ne da zantukan da suke fada shi ya bawa su Asmeer tausayin fatima da baabarta sai suma hawaye ya cika idanuwansu. *** *** *** A can ban garen bakin arne da mai gidansa, bayan bakin arne ya nemo yaran da zai yi aiki da su sai suka zauna suna tattaunawa irin kisar da za suyiwa hajiya da danta. sai wannan mutumin wanda ya saka bakin arne aikin kashe su Asmeer sai ya ce na gano hanyar da za a bi don kashe Asmeer da hajiya cikin sauki, amma kafin ku kashe hajiya sai kun kawo min ita nan gidana ta sai na kawo mata file din da suke guna na babban kamfaninta ta saka hannu sannan ta dakko min duk sauran file din kamfanoninta na nan kasar da na kasashen waje ta saka hannu, baya ga haka sai ta saka hannu a cheque din bankunan da ake ajiye kudaden kamfanoninta, idan ta gama saka hannu kaf sai na kasheta da hannuna sannan na baku gawarta ku je ku jefa a cikin kogi ko ku binneta a wajen da baza a ganku ba. amma kafin kuna kawo min hajiya za ku je ku kama Asmeer ku kashe shi ko ku kawo min shi sannan ku tafo min da fatima. koda bakin arne ya ji haka sai ya ke ce da dariyar mugunta sannan ya ce to ya za muyi da police da suke kula da hajiya da danta? sai wannan wanda ya saka bakin arne aikin sai ya ce su kuma police yanda za a musu shine, kai bakin arne za kayi badda kama ne ka je wajen police da suke kula da hajiya ka ce musu kai daya daga cikin yaran da kuka kayi kokarin kashe hajiya da Asmeer ne sannan kuka kama iyalan likita sai ka ce masa tun kafin police su zo su kama wadanda suka yi kokarin kashe Asmeer da fatima a lokacin da fatima ta kawo Asmeer kuka samu sabani da oganku ka tafi, dan haka kazo ka kaisu wajen wanda ya sakaku ku kashe Asmeer da kuma hajiya to a lokacin za suyi kokarin su kira wasu "yan sanda akan su zo su je tare da su. to kai kuma sai kace masu a"a kar su kira kowa saboda wanda ya saka su yana target din duk wani motsin police dan haka sai su biyo ka ka kaisu, amma sai ka ce musu su cire uniform din su kar wani daga cikin masu lura da motsin police ya gansu, to inhar ya ganku to zai gayawa mai gidanmu. to idan ya gaya masa kuwa zai sa a kashe ku ta yanda ba kuyi tsammani ba. to kana gaya musu haka za su je su cire uniform na su su bika don su je su kama wanda ya saka a kashe hajiya da dansa, domin kuwa duk police suna neman wanda ya saka a kashe hajiya da danta don su samu karin girma. to kai kuma sai ka kaisu can bayan gari ka summace su ka kashe su. to ka ga an gama da police masu kula da hajiya, yaso sai kuje har cikin gidan hajiya ku kamo min ita ku kawo min ita gidana, cikin sauki.amma fa ba da irin shigar nan za kaje wajen police din da shi ba, kaya masu datti zaka saka yanda zasu tabbatar eh kayi kama da mutanen da suka kama a can kauyen su fatima. police masu kula da Asmeer da fatima kuwa da yake duk bayan sallar la"asar idan rana tayi sanyi Asmeer yaka dauki fatima a sabuwar motar da hajiya ta siyawa fatima suna zuwa can filin jirgi yana koya mata mota to sukan tafi da police guda biyu don kula da lafiyar Asmeer da fatima. to sai ku bari sai suna dawo daga filin jirgin idan za su koma gida sai ku tsayar da su. suna tsayawa idan police sun fito sai ku bude musu wuta da bidigogin da zan siya muku, amma shiga za kuyi irin ta miskinai kamar masu neman taimako, to idan kun je kun tsayar da motar su Asmeer din sai kuna cewa fisabilillah! to Asmeer yana da tausayi zai tsaya don ya baku sadaka su kuma police din za su fito don suyi muku masifa su ce ku bar wajen. to ku kuma police din suna fitowa sai ku fito da bindigoginku ku harbe su.bayan kun harbesu sai ku tafo min da Asmeer da fatima nan gidana. sai na hada Asmeer da maifiyarsa na kashe su da kaina ita kuma fatima na mallaketa. amma fa ba a cikin gari za ku tsayar da Asmeer ba a"a a can bayan gari za ku tsayar da su da yake ta bayan garin suke bi. koda bakin arne da sauran yaran suka ji haka sai suka sa ihu suna cewa kai mai gida kana da brain, ai idan ba mai kwakwalwa ba ba yanda mutum zai sai irin wannan hanyar da za abi a kashe hajiya da Asmeer cikin sauki. sai ya dubesu yana murmushi ya ce to yanzu dai gobe za ku je kuyi wannan aikin. sai suka ce mi zai hana yanzu. sai ya ce musu a"a banda yau kam ai yanzu dare ya gabato aikin ba zai yiwu ba. haka da suka kece da dariyar muguta suna cewa gaskiya ne. sai mai gidan nasu ya dakko wani plask wanda siyo abinci a restaurant, da kansa ya shiga kitchen ya dakko plate da kofuna sannan ya dakko joice a cikin firij ya kawo ya zubawa kowa sannan suka hau ci suna hirar kashe Asmeer da hajiya da kuma yanda za su kawowa mai gidansu FATIMA ZAHRA.LOGIN 53 0 68 13 9 6 37 31 40 1 2 2 1 63 3 55 28 8 30 0 51 fufore, adamawa, nigeria Bashir Sani Fesan 闂傚倸鍊搁崐鎼佸磹閹间礁纾归柟闂寸绾惧湱鈧懓瀚崳纾嬨亹閹烘垹鍊為悷婊冾樀瀵顓兼径瀣幐闂佹悶鍎崕閬嶆倶閳哄啰纾奸柣娆屽亾闁搞劏浜幑銏犫攽鐎n偒妫冨┑鐐村灥瀹曨剟宕滈幍顔剧=濞达絽鎼宀勬煕閵娿儳鍩g€殿喖顭锋俊鎼佸煛閸屾矮绨介梻浣侯焾閺堫剛绮欓幋锔绘晜闁跨噦鎷� Home / RAYUWAR FATIMA ZAHRA novels / RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 26 RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 26 Posted by Bashir Sani Fesan on 28 Dec 2016 - 13:50 yadda za su kawowa mai gidansu FATIMA ZAHRA. *** *** *** A can gidan hajiya kuwa lokacin da Fatima ta rungume baabarta tana kuka sai Asmeer da hajiya suka cigaba da tausayawa fatima da baabarta. can zuwa wasu lokuta sai baabar fatima ta janye jikinta daga jikin fatima sannan ta kalleta a lokacin da hawaye yake zuba daga idanuwata sai ta ce godiya ta tabbata ga sarkin da baya barci, mabuwayin kowa da komai, Allah nagode maka da ka hada ni da "yata wacce koda yaushe nake zubar da hawaye saboda ita. yau ga ni ga ta sai hawaye ya kara kwararowa daga idanuwanta. Fatima kuwa gogewa baabarta hawaye take yi tana cewa ki daina zubar da hawaye tunda gani a gare ki, sai ta kama hannunta ta je ta zaunar da ita kusa da hajiya, ita ma a lokacin hajiya ta zauna. sai fatima ta kalli hajiya ta ce hajiya wannan ita ce baabarta wa wacce na sanar da ita a gare ku, sai hajiya ta murmusa ta ce Allah sarki. sai fatima ta kara duban baabarta ta ce baaba amma abun mamaki shine naga kina magana alhalin da baki magana. sai baabar fatima ta ce haka ne kam sai ta gyara zama ta dubi fatima ta ce tabbas da ba magana Amma yanzu cikin ikon Allah ina magana bisa taimakon addu"o"i da kuma taimakon likita. sai fatima ta ja numfashi sannan ta kara kallonta ta ce to amma ya aka yi kika kubuta daga sharrin azzaluman mutanan nan? sannan kuma da irin taimakon da likita ya miki har kika samu lafiyar rashin maganar da kike yi? sai baabar fatima ta ce lokacin da wannan azzaluman mutanen suke tattaunawa yanda zasu kashe ni ne a can wani daki. su basu yi tsammanin ina jin magana ba saboda sun ga lokacin da kike min magana bana miki magana dan haka sai suka yi tsammanain ni kurmiyace bana magana. dan haka sai suke tattaunawar yanda zasu kashe ni. ni kuwa ina jinsu sai kawai na tashi na bi ta taga(window) na gudu. duk galabaitar da nayi na rashin abinci da kuma damuwa bai sa na gagara guduwa ba saboda tseratar da raina. haka na bi ta cikin jeji ina gudu ban ankara ba sai na ga azzaluman mutanan nan suna bina suna cewa na tsaya idan ba haka ba, inhar sun kamani kashe ni za suyi. ni kuwa gudu na cigaba da yi ina neman taimako. to bayan nayi gudu mai nisa wanda ni kaina ban san adadin yawan nisan dayi ba sai kawai na fara gajiya tare da nishi tamkar kirjina zai fito, amma haka na daure na cigaba da kudu. saboda inhar na ce zan tsaya tabbas zasu kama ni. ai kuwa da gudu yayi gudu sai hajijiya ya fara kamani har azzaluman mutanen suka kusa riske ni, abun da bai wuce taku goma su kama ni ba sai na zo tsallaka titi ai kuwa ina zuwa zan zallaka sai naji wani abu ya bige ni. daga nan kuma ban kara sanin inda nake ba sai kashe gari bayan na farfado na ganni akan gadon asibiti. Ashe dai Asmeer ne ya bige ni da mota. bayan na dawo hayyacina sai na ga an daddaure raunukan da na ji. sai na yunkura zan tashi amma na gagara a dole na koma na kwanta. Asmeer da ke bakin gadona sai yake cemin sann sannan yana ce min ki hakuri ki kwanta saboda baza ki iya tashi ba bisa raunukan da ke jikin ki. ni dai ido kawai na zuba masa ina gyada kai saboda ba ni da bakin da zan iya masa magana. shi kuwa bai yi tunanin bani da lafiya ba shi dai a tunaninsa kawai duk zafin ciwo ne ya sanya ni na gagara magana. bayan wasu lokuta sai ga likita ya shigo cikin dakin da nake kwance sai ya zo yayi wasu duba dubansa a cikina sannan ya yi wasu rubutu a cikin wani takarda wanda yake kan durowa a gefena. sannan ya rubuta wasu magunguna a cikin wata takarda ya mikawa Asmeer ya ce wadannan su ne magun gunan da za a siyo. babu wata gardama Asmeer ya karbi takardar ya karanta sunan magun gunan. shi kuwa likita bayan ya mikawa Asmeer takardar sai ya fita yana cewa Allah ya ban lafiya. fitar sa ke da wuya sai Asmeer shima ya fita yana fadin Allah kara min lafiya. sai na gyada kai Alamar Ameen. sannan ya dube ni ya ce zan je na siyo magungunan da likita ya umarce ni na shiyo. da yake ba ni da bakin yi masa magana sai nayi murmushi sannan ya gyada kai. Asmeer kuwa sai ya fita yana fadin Allah kara min lafiya. Haka dai na cigaba da zama ina jinyar jikina Asmeer yana dawainiya a kaina, ya kan yawa min magana amma ni sam bana amsawa saboda bana iya magana har dai ya daina min magana saboda tsammaninsa bana son yawan magana shi yasa ya daina min magana saboda bana miyar masa maganar da yake min. Na kanyi ta kuka idan Asmeer baya nan saboda ba ni da bakin da zan yi masa godiya bisa kulawar da yake ban. haka dai na kasance cikin jinyar jikina har na kai sati biyu. ni kuwa kullum bana rabuwa da addu'o'i da kuma ibadu akan Allah ya ban lafiya game da rashin lafiyar da nake. bayan sati daya ne likita ya lura akan bana iya magana. ranan ya shigo cikin dakin da nake kwance yake ce min ya lura bana iya magana don haka zai duba min mike da muna girgiza kai kawai nayi ina murmushi alamar dai na gode. haka yayi ta dube dubensa irin na likitoti har ya gano cewa rashin maganata ba na cuta ba ce ta asiri ce. haka ya taimaka min ya kirawo wani babban malami ya min addu'o'i sannan ya ban magun gunan da zan ringa sha tare da addu'o'i da zan ringa yi. cikin ikon Allah kuwa bayan kwana biyu bakina ya bude na fara magana. Nayi murna sosai da na ji bakina ya bude wanda ya rufe tun shekaru 8 da suka wuce. kai sai da na gagara yiwa likita goodiya tsabar taimaka min da yayi. shi kuwa Asmeer bai san anyi haka ba. shima kuma likita bai gaya masa ba saboda yayi haka ne saboda Allah. To haka dai na cigaba da jinyar raunukan da ke jikina har na samu lafiya. kullum burina naga na warke na samu gagarumar kyautar da zan yiwa likita da Asmeer amma idan na tuna bani da abun da zan musu sai takaici ya lullube ni. Ranar na Asmeer yazo da wata budurwa ina kwance na juya bayana. sai na ji wannan budurwar ta ce ba baabata ba ce. ina jin muryarki sai na jiyo jiyowar da zan yi sai naga ta fita. amma da yake ba ni da ikon da zan ce ke 'yata ce saboda banga fuskarki ba. sai kawai na danne a raina ban fadawa Asmeer komai ba. amma dai jikina ya ban ke ce. kullum ina son naga kin kara dawowa Amma shiru ban ga kin kara dawowa ba har aka sallame ni na samu lafiya Asmeer ya dakko ni ya kawo ni na yiwa mahaifiyarsa godiya bisa dawainiyar da danta yake min da kuma abubuwan da take kawo min. tun muna bakin asibitin Asmeer yake son ya ji labarina amma na ce ya bari sai mun zauna zan gaya masa. to shine yanzu bayan mun gaisa da hajiya da yi mata godiya sai na budi baki zan bawa Asmeer da mahaifiyarsa labarina da naki sai kuma na jiyo sautin muryarki kin nufo gare ni. Koda fatima ta gama jin dukkanin abubuwan da baabarta ta gaya mata sai ta rungumeta tana kuka. da kyar hajiya da Asmeer da kuma baabarta suka rarrasheta ta daina kuka suna ce mata wannan ai godiya ya kamata kiyiwa Allah ba kuka ba. haka fatima ta share hawayenta. sannan ta dubi hajiya ta kwashe dukkanin abubuwan da suka faru a gareta har ya zuwa yanzu da suke zaune. baabar fatima tayi bakin ciki kwarai da gaske ai kuwa sai ta fara la'antar wadannan azzaluman mutane tare da cewa Allah ya tona asirin duk wanda ya saka su mummunar aiki na kashe hajiya da danta. gabaki daya suka amsa da Ameen. Asmeer da hajiya kuwa murna suka yi sosai game da ganin baabar fatima a gidansu. dan haka sai suka kasance da fatima da baabarta cikin jin dadi da walwala. ai kuwa nan da nan bayan komai ya dawo normal baabar fatima tayi fresh bisa jin dadin da take yi da kuma ta kulawa da hajiya take bata sai ya zamana sun shaku sosai tamkar 'yan uwan juna. suma Asmeer da fatima soyayyarsu ta kafu sosai tamkar wadanda suka dauki shekaru masu yawa suna tare domin kuwa duk inda ka ga Asmeer sai ka ga fatima. har jama.a suke cewa anya wannan ba matar Asmeer ba ce? wasu kuma su ce kodai kanwarsa ce? haka dai suka kasance tare har maganar aka yi maganar aure a tsakaninsu. babu wani bata lokaci baabar fatima ta bawa Asmeer fatima har aka yanke ranar aurensu. [8:09AM, 6/9/2015] Asmeer: *** *** *** Bakin arne da mai gidansa tare da yaran bakin arne kuwa tuni sun gama shiryawa tsaf na kashe Asmeer da mahaifiyarsa hajiya da kuma kamowa Fatima don su kawowa mai gidansu. Koda labarin dawowar baabar fatima ya riski mai gidan su bakin arne tare da saka ranar aure fatima da Asmeer cikin kankanin lokaci sai hankalinsa yayi bala'in tashi. gashi kuma Asmeer da fatima sun daina zuwa filin jirgi don koyawa fatima mota. don haka sai kawai ya ringa zuwa gidan hajiya akai akai don ya jin yanda fatima da Asmeer za su je su don ya samu damar da zai umarci bakin arne da yaransa su aikata abun da suka tsara a baya. Ai kuwa sai ya ji cewa Asmeer da fatima za su je su super market siyowa wasu kayayyake daga cikin kayan aurensu, sannan za su bi ta bayan gari don zagaya gari. sai farin ciki ya kama mai gidan su bakin arne don haka cikin gaggawa ya koma gidansa ya je ya samu bakin arne shi da yaransa ya ce maza ku shirya yanzu ku je ku tari Asmeer da fatima a can bayan gari kuyi dukkanin abubuwan da na ce. amma kai bakin arne gidan hajiya zaka tafi kai tsaye kayi dukkanin abubuwan da na tsara maka sannan ka tafo da hajiya tare da baabar fatima zuwa nan gidana don na aikata abun da nayi niyya sannan na mallaki dukkanin dukiyoyi da kadarorin da mijin hajiya ya mutu ya barwa hajiya da danta. Ai kuwa cikin cika umarni bakin arne suka fita, bakin arne ya je ya dauki mota daga jikin motocin mai gidansa, su kuma yaran bakin arne suka je suka shiga motar da mai gidansu ya siya musu don wannan aikin. sai bakin arne ya nufin gidan hajiya cikin badda kama sannan suma yaran bakin arne suka doshi bayan gari don cika umarnin mai gidan su. Dukkanin abubuwan da mai gidan su bakin arne ya tsara haka kuwa ya afku. Ai kuwa cikin sa'a daya sai ga bakin arne ya shigo da hajiya da baabar fatima cikin gidan mai gidansa duk ya daure hannayensu sannan ya rufe dukkanin bakinsu da fuskarsu da bakin kyalle sannan kuma yana rike da bindiga a hannunsa sai ya shigo da su a lokacin kuwa mai gidan bakin arne yana zaune a kan kujera a cikin falo yana jirana dawowar su bakin arne. ai kuwa yana ganin bakin arne da su hajiya sai ya cika da farin ciki, cikin murmushi yayiwa bakin arne da nuni da dan yatsansa akan ya kai su ciki, cikin bin umarni kuwa ya shiga da su. sai kawai ya je ya bude wani daki na dabam cikin gidan ya tura hajiya da baabar fatima a ciki amma kafin ya tura su ciki sai da ya bude musu dukkanin fuskokinsu. bayan ya saka su a cikin dakin sai ya turo kofa ya rufe. hajiya da baabar fatima kuwa sai kuka suke suna cewa ina ka kawo mu ne kai waye? amma bakin arne ko kula su bai yi ba. sai kawai ya ja kofa ya rufe. Ashe ita baabar fatima ta gane bakin arne domin kuwa shine ogan azzaluman mutanen nan da suka kamata a can kauyen da take da zama. amma sai tayi shiru ba ta gayawa hajiya ba saboda kar hankalinta ya kara tashi. sai kawai ta taya hajiya kuka tare da salati suna neman taimako daga Allah. shi kuwa bakin arne bayan ya tura su hajiya cikin dakin sai ya dawo wajen mai gidansa suka zauna suna jiran zuwa yaran bakin arne da Asmeer da fatima. Suma yaran bakin arne abubuwan da mai gidansu ya tsara musu haka suka bi, sai sai kuma kash! a wajen da suka samu matsala shine lokacin da suke harbe "yan sandan da su tare da su Asmeer. da yake Asmeer da fatima ba su fita a motar ba "yan sanda ne kawai suka bude kofar motar suka fita don yiwa yaran bakin arne wadanda suka yi shigar maroka magana. da fitar su kuwa yaran bakin arne suka bude musu wuta suka harbe su. Ai kuwa Asmeer yana jin karar harbi an harbe "yan sandan da suke tare da su cikin dimaucewa ya danna ribas ta baya har sai da ya taka gawarwakin "yan sanda. babu wata wata ya cigaba da ribas cikin hanzari babu kakkautawa don ya tsiratar da ransa shi da fatima. da yake yaran bakin arne da motar su zo wajen, sun fakata a can wani bangare na daban cikin hanzari suka je suka shiga motar suka bi su Asmeer. Asmeer da ya lura mutanen nan sun biyo su da mota sai ya kara karbin ribas. amma duk da haka sai da wadannan mutanen suka kusan riskarsa duk da tazarar da ya basu a lokacin da ya iyo ribas din saboda mutar mutanen zata fi gudu fiye da ta su Asmeer. Da Asmeer ya ga mutanen sun kusa cimma sai ya dan rage gudu sannan ya juya motar da nufin juyata daga ribas din da yake yi. ai kuwa yana juya ta sai ya ji motar ta mutu bisa rashin mai. domin kuwa tun suna super market Asmeer ya lura babu mai a motar amma ya bari idan ya je gidan mai wanda yake can bayan gari sai ya sha. koda Asmeer ya ji motar ta mutu sakamakon babu mai. sai ya fita a motar sannan ya umarci da fatima su gudu su shiga jejin da yake tsalleke da titin amma sai fatima ta ce kazo mu bi titi mana watakil mu samu wanda zai taimaka mana cikin daka tsawa ya ce ya za mu bi titi kai tsaye ai idan mun bi titin za su ji dadin kama mu. ai kuwa suna cikin haka sai Asmeer ya hangi wadannan mutanen da suke binsu sun kusan karisowa. cikin hanzari Asmeer ya finciki hannun fatima ya ja ta da gudu suka lallaka cikin jejin da yake gefe da titin. haka suka nausa ciki suna gudu. su kuwa wadannan mutanen da suka kariso wajen motar su Asmeer sai suka faka a gefe domin kuwa tun daga nesa sun hangi Asmeer da fatima sun fita a motar sun shiga cikin jeji. ai kuwa suna karisowa wajen motar su Asmeer sai dukkaninsu suka fice a motarsu suka bi bayan Asmeer da FATIMA ZAHRA.MA ZAHRA novels / RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 27 RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 27 Posted by Bashir Sani Fesan on 28 Dec 2016 - 13:53 Asmeer da fatima gudu suka cigaba da yi a cikin jejin babu kakkauta. su ma kuwa yaran bakin arne cigaba da bin Asmeer da fatima suka cigaba da yi. suna rike da bindigogi. da yake su Asmeer sun basu tazara sosai sai daya daga cikin yaran bakin arne ya daga murya ya ce ku dakata idan ba haka ba kuwa za mu harbe ku. Asmeer da fatima kuwa gudu suka cigaba da yi basu tsaya ba. haka dai yaron bakin arnen ya cigaba da cewa inhar baku tsaya ba fa za mu harbe ku. gudu da yayi gudu sai fatima da fara haki tana cewa brother na ga ji fa. sai Asmeer ya ce ki daure dai nasan baza a rasa wani dan karamin kauye a nan gaban mu ba. haka dai ta daure suka cigaba da gudu sai dai kuma Asmeer ya wuce ta saboda fatima ta ga ji sosai saboda gudun da suke yi, sai Asmeer yake ce mata ga su can fa suna kokarin kama mu ki kara gudu fa. ita kuwa fatima sai haki take yi. koda gudun ya yiwa fatima yawa sai kawai ta daina gudu tana sassarfa sannan tana haki tamkar kirjinta zai tsage. muryarta a shake take cewa Asmeer wallahi na ga zuciya ta zata fito. sai Asmeer shima ya rage gudu yana haki yana cewa kanwata ki kara daurewa dai idan sun kama mu fa kashe mu za suyi saboda sun harbe "yan sandan da suke kula da mu. dan haka ki hakuri ki kara gudu mu dan kara gaba ko Allah zai sa mu riski kauye a gaban mu. Da kyar fatima da dan kara gudu koda ta yi dan kara min gudu sai kawai jiri ya debeta ta fadi kas tana haki tana cewa wayyo Allah na zan mutu. Asmeer yana ganin fatima ta fadi sai ya tsaya sannan ya durkusa a gabanta yana haki yana cewa ki daure ki tashi mu gudu ga su can fa sun tun ka ro mu. fatima tana daga kwance cikin shashshakar murya tare da nishi ta ce brother na wallahi bazan iya cigaba da gudu ba kirjina yana bugawa tamkar zai tsage sai kawai ta fashe da kuka ta ce brother na ka gudu ka tseratar da ranka, ka bar ni su zo su kashe ni, kai dai ka gudu ka tseratar da ranka, ni dai tawa ta zo karshe, sai kawai ta kara fashewaa da kuka Babu zato babu tsammani sai hawaye suka kwararo daga idanuwan Asmeer ya ce haba! mi yasa ki ke cewa haka. bazan iya guduwa na barki a nan ba balantana har su zo su riske ki a nan. Su kuwa masu bin su Asmeer koda suka ga fatima ta fadi a kas sannan Asmeer ya tsaya sai suka cika da murna suna cewa yauwa ga su can sun tsaya maza mu kara gudu muje mu kama su, ai kuwa sai suka kara kaimin gudunsu. Asmeer yana daga durkushe a gaban fatima yana cewa ta tashi su gudu sai kawai ya hango mutanen da suke binsu sun kusa cimma musu, a kidimauce Asmeer ya kama hannayen fatima ya tayar da ita sannan ya kamo kugunta sannan ya dora hannunta na dama ya dora a kafadarsa sannan ya ja ta da kyar ya tallafa mata suka tafi. Da yake sun zo daf da wata duhuwa sai kawai Asmeer ya ja fatima suka shiga cikin duhuwar jejin. Mutanen da ke biye da su kuwa koda suka zo daf da wajen duhuwar da su Asmeer suka shiga sai suka tsaya cak suna dariyar mugunta suna cewa ai gudunsu ya kare. sai daya daga cikin yaran bakin arne ya ce mutum biyu su shiga ciki su duba su sannan su fito da su. mu kuma za mu tsaya a nan idan munga sun fito sai mu kama su. hakan kuwa aka yi sai mutane biyu suka shiga ciki suna duba su. Abu kamar wasa sai suka nemi su Asmeer sama da kasa suka rasa, har suka fara gajiya da nemansu wadanda suke wajen duhuwar sai suma suka shigo ciki su ka cigaba da neman su Asmeer amma shiru ka ke ji " wai malam ya ci shirwa." sai da suka doke rabin sa'a suna neman su Asmeer amma ba su same su ba har suka fara shawartawa su koma kawai. Asmeer da fatima kuwa suna can ciki sun shiga cikin wani sarkakiya ida babu wanda zai iya ganinsu saboda duhun wajen. da yake fatima tana nishi sosai sai Asmeer ya ce ta rufe bakinta kar su jiyo sautin numfashinta haka fatima da rufe bakinta sannan ta sassauta jan numfashinta. suna wajen suna la6e sai suka jiyo muryar mutanen suna cewa mu tafi kawai don baza mu samu su ba. da ya ke mutanen sun rarrabu ne sannan kuma akwai daya daga cikin su wanda yake kusa da su Asmeer amma baya ganinsu saboda suna cikin duhu sai kawai ya juya zai tafi ya bar wajen. Su Asmeer kuwa suna ganin duk zirga zirgan da suke yi. to da wannan wanda yake kusa da su ya juya zai tafi sai fatima ta yi arba da mummunar fuskarsa bata san lokacin da ta bude baki za tayi kara ba. cikin zafin nama Asmeer ya yi farat ya rufe mata baki. amma duk da haka sai da sautin karar ya fito. ai kuwa sai wannan wanda yake kusa da su Asmeer sai ya juyo da sauri ya nufi wajen da sautin karar ya fito ai kuwa yana zuwa daf da wajen sai ya ga karangiya talullube wajen sai kawai ya yaye karangiyar. ai kuwa yana yayewa sai ga Asmeer da fatima a tsaye a wajen suna muzurai da idanuwansu. fatima jikinta sai rawa yake yi. [9:12AM, 6/12/2015] Asmeer: Sai kawai yayi kuruwa ya budi baki ya ce ku zo ku ga....kafin ya karisa sai Asmeer ya dunkule hannunsa ya zabga masa naushi a fuska, sai jini yayi tsurtuwa daga fuskarsa nan da nan kuwa ya cilla wani ihu sannan ya fadi kasa sumamme. su kuwa sauran yaran bakin arne ashe sun ji kuruwar da daya daga cikinsu yayi ai kuwa sai suka nufo wajen da suka ji ihun daya daga cikin su. Asmeer kuwa bayan ya naushi wannan mutumin sai ya kama hannun fatima ya ja ta suka bar wajen da gudu amma ina gudunsu duk a banza domin kuwa tuni wadannan mutanen sun riske su sai kawai daya daga cikin mutanen ya yi nuni da bindigarsu a Asmeer ya ce ku dakata ko na harbe ku. koda Asmeer ya ga anyi terget nasu da bindiga sai Asmeer da fatima suka tsaya cak. sai su ma wadannan mutanen suka tsaya sannan suka kewaye su Asmeer. sai daya daga cikinsu ya fashe da dariya ya ce kun gama gudunku mun kama ku dan haka ku wuce mu fita daga cikin duhuwar nan sannan mu aikata abun da aka umarce mu mu aikata. sai Asmeer yayi musu wani irin kallo na reni sannan ya fara wani irin huci tamkar zaki a cikin dawa. suna jin hucin da Asmeer ya ke yi sai suka razana ainin suka fara kallon kallon a Asmeer. sai daya daga cikin su ya biyo ta bayan Asmeer da nufin ingizashi su tafi. ai kuwa yana taba Asmeer. cikin zafin nama Asmeer yayi wani kuruwa ya sure shi ya makashi da kasa sai jini ya fara malala daga hancinsa da bakin sai shima nan take ya suma. sauran mutanen suna ganin haka sai suka tsoruta da Al"amarin Asmeer sai suka ce a ransu anya wannan mutum ne? sai suka fara ja da baya. su har sun manta suna rike da bindigogi. sai daya daga cikin su ya kalli Asmeer ya kai ka wuce mu tafi cikin salama idan ba haka ba kumamu harbeka a nan. sai Asmeer ya kalli wanda yayi managar ya ce da shi ku su waye? sannan waye ya aiko ku ku kashe mu? sai daya daga cikinsu ya ce mai gidan mu ne ya umarce mu mu zo mu aikata kisa a gare ka sannan mu tafi da wannan budurwar wacce kake tare da ita dan haka ka wuce mu tafi. suna cikin haka sai daya daga cikinsu ya lallabo ta bayan Asmeer ya biga masa kasin bindiga. buga masa da yayi ne ya sanya Asmeer ya fadi kas sumamme. ita kuwa fatima sai ta calla wani uban ihu ta ce wayyo sun kashe min dan uwana masoyina sai kawai ta durkusa a gaban Asmeer tana kuka. su kuwa mutanen sai suka kece da dariyar mugunta sannan daya daga cikin su ya umarci daya daga cikinsu ya dauki Asmeer su fita da shi daga cikin duhuwar jejin. cikin cika umarni kuwa suka ture fatima suka cincibi Asmeer suka fita da shi sannan suka angiza fatima wacce take ta rusa kuka suka fita da ita daga duhuwar jejin. Bayan sun fito ne sai daya daga cikin su ya dakko waya daga aljihunsa ya kira mai gidansu sai ya ce ranka dade ga su nan a hannun mu fa mun kama su har mun sumar da Asmeer saura mu kashe shi kawai. sai mai gidan ya ce ina fatan bai mutu ba sai ya ce eh ranka dade bai mutu ba sai ya ce mu su yauwa to kar ku kashe shi ina son na kashe shi da hannuna saboda kafin ya mutu akwai abubuwan da nake so na ce masa dan haka ku kwatanta min dai dai wajen da kuke sai na zo ni. sai ya kwanta masa wajen sannan ya ce idan kazo zaka ga motarmu da tasu a gefen titi to sai ka tsallo ka shi domin kuwa sun gudu ne kafin mu kama su. sai mai gidan nasu ya ce to gamu nan muna zuwa da bakin arne. sai ya ce ranka dade sai kun zo. Abun da bai wuce rabin sa"a ba sai suka iso wajen shi da bakin arne. fatima tana zaune a kusan Asmeer da yake a lokacin Asmeer ya dawo daga dogon suman yake. Asmeer yana ganin ganin wannan mutumin wanda ya saka wadannan mutanen don su kashe Asmeer Ashe shine manajan babban kamfanin mahaifiyarsa. Asmeer da fatima suna ganinsa sai suka mike cikin murna suna cewa yauwa manaja kwanda da kazo sai suka je suka tsaya a bayansa suna cewa ka taimaka mana za su kashe mu. Manajan yana jin haka sai ya kece da dariyar mugunta sannan ya jawo Asmeer daga bayansa ya kwashe shi da mari ya ce waye zai taimake ka? Ai ni nasa A kashe ka sannan a tafo min da fatima don na aureta, yanzu haka uwarka da baabar fatima suna hanuna zan kashe uwarka wato hajiya ita kuma baabar fatima da yake sirukata ce bazan kashe ta ba. sannan yanzu haka dukkanin kadarorin da mahaifinku da ya bar maka suna hanuna kudaden da suke cikin bank na kune kawai ba su zo hanuna ba saboda da sign naka ake fitar da kudade daga bank dan haka shine nazo wajenka kasa min hannu don na mallaki tarin dukiyar da ke cikin bank na ku.... kash! mu hadu a part 28 don jin cigaban labarin.A novels / RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 28 RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 28 Posted by Bashir Sani Fesan on 28 Dec 2016 - 13:55 Koda Asmeer da fatima suka ji dukkanin abun da manaja ya fada. sai suka ja baya. sai Asmeer ya ce mi kake fada ne haka manaja? sai maja yasa dariya sannan ya kara da cewa abun da ka ji na ce shi nake nufi sannan ka sa ni tun lokacin da nake tare da mahaifinka nake rena abun da yake ban sannan kuma nake bin duk hanyar da zan bi da zan mallaki wani abu daga cikin dukiyar mahaifinka bari ka ji ma nine sanadiyar mutuwar mahaifinka da kanwarka domin kuwa ni nasa a kunce masa birkinsa na mota a lokacin da zai kai kanwarka airport, daman koda yaushe ina neman hanyar da zan bi don kashe haifinka da mahaifiyarka da kai kanka amma ban samu damar hakan ba a kanka kai da mahaifiyarka sai wannan lokacin. ka sani ni na saka a kama baabar fatima dan fatima ta je ta sa muku guba a abinci ku ci ku mutu. sannan ni na sa a kama iyalen likita duk dai don na ga bayanku kai da mahaifiyarka sannan kuma ni nasa a kashe wadannan yaran bakin arne da aka kama a police station gudun kar su tona min asiri, an kashe su ne bisa taimakon daya daga cikin police wanda yanzu haka baya garin. koda manaja ya zo nan a bayaninsa sai ya numfasa sannan ya cigaba da cewa duk da irin tarkon da na kafa muku kai da mahaifiyarku ban samu damar ganin bayanku ba Allah yana taimakonku, sai yanzu ne na samu nasarar kama ku kai da mahaifiyarka. bugu da kari rannan bayan na shigo gidanku muna zaune da mahaifiyarka sai kuka dawo daga super market kai da fatima to lokacin da ta gaishe nine na ji na kamu da tsananin sonta kuma nake burin na cimma burina a kanta koda kuwa ba aurenta zan yi ba, daman ka sanni da neman matan banza, don haka ita ma fatima ta shiga jerin matan da zan so naga nasan ita mace ce kuma fatima zuciyata ta.....kafin ya karisa maganarsa sai Asmeer ya daka masa tsawa nan da nan kuwa idanuwansa suka yi ja cikin bacin rai ya kalli manaja ya ce kai maciyin amana ne azzalumi, fasiki wanda bai sannan halacci ba. dukkanin abubuwan da iyayena suke maka baza ka saka musu da komai ba sai da cin amana da zalunci. to ka sani Allah ya fika koma shi zai rusa maka dukkanin makircin da ka shirya a kanmu...sai kawai ya fashe da kuka cikin sassanyar murya ya cigaba da cewa dan Allah ka taimaka min kar ka kashe mahaifiyata sannan kar ka lalata kanwata fatima inhar za kamin haka na yarda ni ka kashe ni ka barsu. koda manaja ya ji haka sai ya fashe da dariyar mugunta sai suma yaran bakin arne da shi kansa bakin arne suka kece da dariyar mugunta. ita kuwa fatima fashewa tayi da kuka tana cewa dan Allah kayi hakuri manaja. bayan sun gama dariyarsu sai manaja yayi murmushi ya ce na yarda zan bar mahaifiyarka a raye sannan bazan taba lalata fatima ba amma kafin nayi haka sai ka saka hannu a cikin takardun bank naku sai ya dakku wasu takardu daga aljhunsa ya mikawa Asmeer ya ce ga su nan kasa hannu. jikin Asmeer na rawa ya karbi dakardun da biro. sai fatima ta fashe da kuka tana fadin kar kasa hannu yayana yaudararka zai yi. shi kuwa Asmeer bai kulata ba ya saka hannu a dukkanin takardun sai ya mikawa manaja. koda manaja ya karbi takardun sai ya sumbaci takardun yana dariya sannan ya ce yes yansu komai ya zo hannuna. sai ya miyar da takardun cikin aljihunsa sannan ya juya kan yaran bakin arne ya ce maza ku dakko igiya a cikin motarku ku zo ku daure Asmeer da hannuna zan kashe shi. haka kuwa aka yi suka zo suka daure Asmeer sannan da kansa manaja ya dakko wata igiya ta dabam ya shake wuyan Asmeer da nufin ya kashe shi. ita kuwa fatima tana ganin ha sai ta cilla ihu tana kuka. bata da damar ceton Asmeer saboda duk sun fita karfi tana gani Asmeer idunuwansa suka zazzago tsabar azaba. abun da bai wuce minti buyu ba sai Asmeer kafafunsa suka sandare sannan jikinsa ya sake alar ransa ya fita. koda manaja ya ga haka sai ya tabbatar Asmeer ya mutu. sai kawai ya sake shi. sai Asmeer ya fadi kas alamar ya mutu. [10:46AM, 6/13/2015] Asmeer: fatima tana ganin haka sai ta cilla ihu sannan ta fadi kas sumammiya. Haka manaja da bakin arne tare da yaran bakin arne suka bar waje tare da fatima suka bar gawar Asmeer a wajen. Bayan rabin sa'a da afkuwar haka sai ga wasu mutane su biyu kowannansu akan jaki. bayan sun zo daf da inda Asmeer yake kwance sai suka cika da mamaki sai suka fara juye juye suna duba ko akwai wasu mutane a kusa amma basu ga kowa ba. haka suka kariso wajen da Asmeer ke kwance. suna zuwa wajen sai suka ce kai gawar mutum ne a wajen maza mu bar waje. sai suka juya da nufin guduwa sa suka ga Kafar Asmeer na motsi. sai suka kalli junansu suka ce ashe ba mtuwa yayi ba. to amma mi yasa me shi? sai suka rasa amsar da za su bawa kansu. sai daya daga cikin su ya ce maza mu dauke shi mu tafi da shi don yana bukar taimako haka suka dorashi akan jaki suka tafi da shi can rigarsu da yake daman sun fito ne don yin ita ce sannan dukkaninsu manya ne domin kuwa a kalla sun kai shekaru 5O. cikin gaggawa suka je suka kwantar da shi suka kawo masa ruwa da kyar suka bashi ya sha abun da bai wuce dakika 120 ba sai Asmeer ya dawo hayyacinsa. "Ashe lokacin da manaja ya shakewa Asmeer wuya da Asmeer ya tabbar kashe shi zai yi sai kawai Asmeer ya saki jikinsa tamkar ya mutu.".A ZAHRA novels / RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 29 RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 29 Posted by Bashir Sani Fesan on 28 Dec 2016 - 13:57 Asmeer ya razane ya tashi, yana tashi kuwa ya ganshi a gaban wadannan mutane guda biyu wadanda suka kawo shi. sai kawai ya fara cewa karka kashe min momi na! manaja. koda suka ji abun da Asmeer ya fada sai suka kalli junansu suna mamaki. sai Asmeer ya kalli wadannan mutanen ya ce ina nake ne? sai suka ce kana rugar fulani ne wacce take yamma da garin kano. yana jin haka sai ya mike cikin sauri yana cewa ku taimaka min ku kai ne cikin kano na je police station na yi musu report sai mu je gidan manaja don na kubutar da mamana da fatima da kuma baabar fatima. koda su ka ji abun da Asmeer ya fada sai suka cika da mamaki suka ce mi yake faruwa ga su maman naka? sai Asmeer ya ce ku dai ku kai ni ba sai kun ji ko miye ba. sai daya daga cikinsu ya ce kata yayi ka gaya mana ko mike faruwa ko muma akwai taimakon da za muyi maka. da Asmeer dai ya gq cewa idan bai fada musu duk abun da yake faruwa ba za su 6ata mishi lokaci sannan manaja zai iya aikata abun da ya ce zai aikata akan mahaifiyarsa da abun begensa Fatima, cikin sanyi jiki ya zauna sannan ya nutsu a lokacin hawaye sun cika idanuwansa. sai ya kalli wadannan mutanen ya ce tabbas inhar ban hanzarta zuwa police station nayi report ba sannan mun je gidan manaja ba babu shakka manaja zai aikata abun da ya furta zai aikata. sai Asmeer ya kwashe dukkanin abun da ya faru a gare shi da mummunar manufar da manaja yake son ya samu a kansa da mahaifiyarsa tare da fatima ya zayyana musu. sannan ya sanar musu shi dan marigayi Alhaji ibrahim dan kasuwa ne. Koda suka ji dukkanin labarin Asmeer da kuma jin cewa shi dan marigayi Alhaji ibrahim dan kasuwa ne sai suka cika da mamaki da tausayin Asmeer saboda sun san mahaifinsa sosai saboda ya shahara a kano wajen kasuwanci. dan haka sai daya daga cikinsu ya ce zan taimaka maka na kaika har cikin garin kano sannan da ni za a je har police station kayi report ga "yan sanda don ceton mahaifiyarka. suna cikin maganan ne sai Asmeer ya lura cewa daya mutumin wanda yake zaune a kusansu yana zubar da hawaye. sai Asmeer ya cika da mamaki ya ce wannan dan uwan naka yana ga yana zubar da hawaye.? sai dayan ya ce eh haka yake kuka duk lokacin da ya ji an ambaci fatima saboda sunan matarsa fatima sunan "yarsa ma fatima su yake tunowa sannan da abun da ya same shi, kaima da yake ka ambaci fatima a cikin zantukanka shi ya saka shi kuka. sai Asmeer ya ce Ayyah! mi ya samu matar ta sa da "yarsa? sai ya ce duk Allah ya musu rasuwa. sai Asmeer ya ce Ayyah Allah ya ji kansu da rahma sai ya ce Ameen. sai Asmeer ya ce to amma na ga gidan kamar ba kowa? sai wannan mutumin ya ce eh matan gidan sun tafi debowa ruwa a rafi. sai Asmeer ya numfasa ya ce to gaskiya ya kamata mu hanzarta tafiya zuwa cikin gari kar lokaci ya wuce. sai Asmeer ya mike sai shima mutumin ya mike sannan ya shiga cikin daki ya dakko sanda da butar ruwa. bayan ya fito ya kalli dayan dan uwan nasa ya ce abokina kamal kai ka tsaya a gida idan su yalwaji sun dawo daga diban ruwa ka ce musu na shiga gari zan dawo kafin faduwar rana. sai kamal ya mike tsaye yana goge hawayen da ke zuba daga idanuwansa ya ce iro kaima kasan dole na bi ku na je na taimaki mai sunan "yata kuma mai sunan matata. sai iro ya numfasa ya ce kai hakuri ka ga babu kowa a gidan sannan dole ka je jeji ka iyo itace saboda kasan ba muyi ba. sai kamal ya ki fir haka dai iro ya hakura suka je har bakin rafi suka samu matan gidansu suka sanar musu komai sannan suka ce da su idan sun gama diban ruwan sai kuyi hakuri ku je ku iyo itace. sai suka ce to babu komai. haka su uku suka tafi suka nufi cikin garin kano. [7:55AM, 6/14/2015] Asmeer: Koda suka isa cikin kano ba su tsaya bata lokaci ba suka nufi police station suka yi report ga "yan sanda sannan Asmeer ya zayyanawa "yan sanda komai da komai har da hada bakin da akayi da police aka kashe yaran bakin arne wadanda aka kama su. Ai kuwa nan da nan police suka cika helux na su na police tare da Asmeer da wadannan mutane biyun da suka rako Asmeer aka nufi gidan manaja. *** *** *** Shi kuwa manaja da bakin arne tare da yaran bakin arne lokacin da suka dawo gida sai aka je aka ajiye fatima a dakin manaja a lokacin da take halin suma. sannan ya sa aka fiddo da hajiya daga dakin da aka tsare ta ita da baabar fatima. bayan an fito da su sai aka kawo su cikin falonsa aka jiye su. sai manaja ya zo ya zauna yana ta kecewa da dariya sannan ya dakko dukkanin takardun kamfanonin mijin hajiya da dukkanin kadarorinsa na gidaje da filaye da sauran kadarorinsa ya ajiye a gabansa sannan ya cigaba da dariya. bakin arne da yaransa suma dariyar muguntan suka taya manaja babu kakkautawa, zuwa wasu lokuta sai manaja ya daina dariya sannan ya kalli hajiya lokacin ya ce hajiya khadija matar marigayi Alhaji ibrahim dan kasuwa. ita kuwa a lokacin kuka take yi tana ta ambaton ina danta da fatima suke??? ita kuma baabar fatima tayi kukan har ta ga ji sai kawai ta sunkuyar da kanta dukka idonta suyi jajawur sannan sun kumbura sai ambaton Allah take yi tana neman agajinsa da ya kubutar da su daga cikin halin da suke sannan ya kare mata "yarta fatima a duk inda take. shi kuwa manaja sai ya cigaba da cewa hajiya ki daina damuwa akan danki Asmeer domin kuwa tuni na gama da shi, ita kuma fatima tana dakina a sume idan ta dawo hayyacinta za a daura mana aure, kinga ga tarin dukiya ga kuma auran fatima. a kidimauce hajiya ta dago da kanta ta ce to tunda ka gama da Asmeer sai ka kawo min shi na ganshi shi da fatiman. sai manaja ya fashe da dariya ya ce ba haka nake nufi ba ina nufin danki Asmeer na kashe shi. wani ihu hajiya tayi sannan ta rike kanta sai ta ce karya kake manaja baka isa ka kashe dana ba. dana baya mutuwa. sai manaja da bakin arne da sauran yaran bakin arne suka zurawa hajiya ido domin kuwa irin abubuwan da take ambata da kuma irin yanayin da take yi shi suka tabbatar musu hajiya ta samu tabuwar hankali (ta zama mahaukaciya). sai hajiya ta cire dankwalin da ke kanta tana cewa karya kake manaja dana ba za ka iya kashe shi ba, Asmeer ba zai mutu ba. baabar fatima tana ganin irin abubuwan da hajiya take yi sai ta riketa tana kuka tana cewa hajiya ki hakuri. amma hajiya kuwa dariya ta ke yi sai ta kalli baabar fatima ta ce ko kema kin yarda da na Asmeer ya mutu. sai baabar fatima ta biye ta ta ce a'a ban yarda ba. sai hajiya ta cigaba da dariya irin ta mahaukata tana cewa dana Asmeer bai mutu ba, idan kuma ya mutu nima mutuwa zanyi sai da fadi a jikin baabar fatima sannan ta ce yuuuu nima na mutu. baabar fatima kuka ta cigaba da yi sannan ta dago da kanta ta kalli manaja ta ce kayi asara wallahi ai hajiya ta gaya min kai ne babban manajanta wanda ta yarda da kai fiye da sauran ma'ikatanta na kamfanoni sannan take burin ta mallaka maka kamfanin da kake kula da shi, amma babu abun da zaka saka mata da shi sai da cin amana da zalunci wallahi wadaran da kai, ka cuci hajiya kuma Allah ba zai taba barinka ba a fadin duniyar nan. kasani duk dukiyar da ka rike da kadarorin da ka rike duk na maraya ne wato Asmeer. kuma Allah baya barin duk wanda ya ci dukiyar maraya ko a wuta ma shi wutarsa dabamce, kuma fatima 'yata da ka ce zaka aure ta insha"Allah Allah ba zai baka damar ka aure ta ba domin kuwa duk wacce ta aure ka tana cikin masifa da bala"i. koda manaja ya ji abubuwan da baabar fatima take cewa sai ya daka mata tsawa sannan ya ce kema kin ci sa'a dan ke baabar fatima ce da dake zan hada duk na kashe. yana gama fadin haka sai ya umarci daya daga cikin yaran bakin arne da ya dauki su baabar fatima ya miyar da su ciki, kafin ya je ya kashe hajiya. haka yaron bakin arne cikin tsawa ya umarci baabar hajiya da ta tashi ita da hajiya su tafi dakin da aka dakko su. haka baabar fatima ta rungumin hajiya ta ja ta suka nufi dakin da aka dakko su. ita kuwa hajiya har a lokacin lau lau take da kanta sannan ta rufe idonta tana cewa nima na mutu. har aka je aka rufe su a dakin da aka dakko su. shi kuwa manaja kwalbar giya ce a gabansa sai ya dakko kofi da ke gabansa akan tebur sannan ya zuba a kofin ya fara sha. sannan ya dakko akwati a gefensa ya ajiye a gabansa sannan ya kalli bakin arne ya ce yauwa babban yaro na ka gama aikinka dan haka ga kudaden da na ce zan baka kai da ya ranka. sai manaja ya bude a kwatin sai ga dumin dumin "yan dubu dubu a jere a ciki. bakin arne da yaransa zare idanuwa su kayi sannan suka hadiyi yawu sai suka ce wow! sai suka sau murmushin murna. sai manajan ya rufe a kwatin sannan ya mikowa bakin arne sai bakin arne ya mika hannu zai kar6i kudin, kafin ya kar6a sai suka ji ana kwankwasa kofan falon sai manaja ya ce waye? sai ya ji muryar mai gadinsa ya ce nine ranka dade. sai manaja ya ce mi ya kawo Kawo nan mai gadi sai ya ce sako aka ban na kawo maka. sai manaja ya umarci daya daga cikin bakin arne da ya je ya bude kofar falon. Ai kuwa yana budewa sai police suka yi farat suka shiga ciki sannan suka nuna su da bindigogi suka ce all u are under arest.FATIMA ZAHRA novels / RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 30 the end RAYUWAR FATIMA ZAHRA part 30 the end Posted by Bashir Sani Fesan on 28 Dec 2016 - 14:00 Bayan anyi aresting din su manaja sai Asmeer ya je ya cakumi rigar manaja ya ce ina mamana da fatima tare da baabarta? cikin manaja yana karkarwa ya nuna dakin da ya kai hajiya da baabar fatima. cikin sauri Asmeer ya ruga da gudu zuwa dakin da aka rufe hajiya, yana zuwa sai ya tura kofar amma sai ya ji kofar a kulle, dawowa yayi da gudu ya zo ya samu manaja ya ce ina makullin dakin? sai manaja ya nuna yaron bakin arne wanda makullin yake hannunsa a kidimauce Asmeer ya je ya karbi makullin dakin. yana bude dakin sai ya ga baabar fatima tana ta kuka sannan tana d addu"o"i. ita kuwa hajiya a lokacin idanuwanta a rufe suke tana ta sumbatu irin na mahaukata. Asmeer yana bude kofar dakin. koda baabar fatima ta ga Asmeer sai ta mike tsaye tana murna. cikin murna ta tayar da hajiya tsaye. da sauri Asmeer ya zo ya ce mi ya samu hajiya? sai baabar fatima ta fashe da kuka ta ce bata da lafiya ne sakamakon jin manaja ya kashe ka. da Asmeer ya ji haka sai ya kama hannun hajiya ya ce momi gani nan ban mutu ba. koda hajiya ta ji muryar da ta sai ta zabura sannan ta bude idanuwanta tana dariya ta ce dana daman na ce musu baza ka mutu ba, sai ta kalli baabar fatima tana dariya sai ta ce kin ganshi nan bai mutu ba ya mutu ya dawo. koda Asmeer ya ga irin abubuwan da hajiya take yi sai ya tabbatar har yanzu hajiya bata dawo hankalinta ba sai kawai hawaye suka kwararo daga idanuwansa. sai kuma ya waiga gefe da gefe cikin dakin yana cewa ina fatima? sai baabar fatima ta ce na ji manaja ya ce tana dakinsa a sume jikin Asmeer a sanyaye ya ce to kamamin hanun hajiya mu fita da ita. sai suka kama hannayen hajiya suka fita da ita zuwa falo. koda suka fito falon sai suka je suka zaunar da hajiya akan kujera, suna ajiyeta kuwa Asmeer a fusace ya nufi wajen manaja, yana zuwa gabansa ya dauke shi da mari ji kake tassss.... a dai dai lokacin hawaye suka kara kwararowa daga idanuwan Asmeer sannan ya ce ka cutar da mahaifiyata ka zalunceta ka kashe min mahaifiya wallahi bazan taba yafe maka ba. jin abun da Asmeer ya fada ne ya sanya dukkanin police din waje suka zare idanuwa da cewa haba Asmeer kai hakuri mana. suma wadanda suka rako Asmeer suma bakunansu suka rufe suna mamakin abun da Asmeer ya fada. shi kuwa manaja babu abun da ya ce sai kawai ya sunkuyar da kansa jikinsa na karkarwa. sai Asmeer ya ce masa ina ne dakinka maza ka je ka bude ka fito min da fatima. a dai dai lokacin ne suka ji ana ta buga kofar daki a bayansu, sai Asmeer ya ji muryar fatima tana kuka tana cewa a taimake ni. cikin sauri Asmeer ya cewa manaja ina makullin dakin da fatima take bugawa? jikin manaja yana karkarwa ya sa hannu a aljihunsa ya dakko makullin dakin ya mikawa Asmeer. sai Asmeer ya karbi makullin ya je ya bude dakin. koda fatima ta ga Asmeer ne ya zo ya bude ta sai ta yunkura zata rungume shi tsabar murna sai Asmeer ya ce dakata miye hakan ni ba muharraminki ba ne. sai jikin fatima yayi sanyi sai ta kawar da kanta tsabar kunya. kawar da kan da tayi ne ta hango baabarta zaune kusan hajiya tana murmushi bisa ganin fatima. sai fatima ta rugo a guje ta zo ta rungumeta tana kuka. ita kuwa baabar fatima sai ta shiga rarrashin fatima a lokacin ne baabar fatima ta hada ido da khamal wato daya daga cikin mutanen da suka rako Asmeer sai kawai ta janye fatima daga jikinta sannan ta tashi cikin sayin jiki ta je ta tsaya a gaban khamal. ita kuwa fatima bin baabarta kawai tayi da kallo tana mamaki. [8:31AM, 6/16/2015] Asmeer: koda baabar fatima ta tsaya a gaban khamal sai ta ce kamar khamal mahaifin fatima nake kallo. cikin mamaki khamal ya ce eh nine, sai shima ya ce wannan kamar rabi mai aiki nake gani?? sai baabar fatima ta ce nine khamal. sai kamal ya cika da mamaki. sai baabar fatima ta ce daman baka mutu ba lokacin da Amaryarka ta soka maka wuka? sai hawaye suka cika idanuwansa ya ce eh ban mutu ba domin kuwa lokacin da ta caka min kuwa sai ta biki a guje bisa ganin kin gane ta. to da yake a lokacin ban fita daga hayyacina ba sai na kira wayar iro abokina wato wannan wanda kike ganina tare da shi. ina kiransa a waya sai na sanar masa halin da nake ciki. yana kasuwa wajen kasuwancinsa ya zo a guje ya taimaka min ya kaini asibiti. bayan an sallame ni a asibiti sai ya dauke ni zuwa gidan da suke kwana. ita kuwa amaryata da ta dawo bata gani ba sai hankalinta ya tashi sai ta shiga binciken yanda nake har ta gano ina gidan da abokina iro yake haya. sai kawai tasa "yan daba su zo su kashe ni. ai kuwa cikin dare aka shigo gidan daman da yake gidan duk maza ne babu mace ko daya kuma daman a lokacin iro bai yi aure ba. to kuma dukkanin mu a tsakar gida muke kwana da yake lokacin zafi ne kuma babu wuta a gida. wadannan "yan daban suna shigowa sai suka rasa a inda nake domin kuwa mutanen gidan suna da yawa kuma an babbazu a filin gidan ana ta bacci. suna shigowa sai suka yanke shawara su kashe duk wanda tsautsayi ya hau kansa domin kuwa baza su gane ni ba kuma idan sun koma za suyi asarar kudin ta amaryata ta ce zata ba su. haka suka kashe daya daga cikin gidan suka je suka cewa hajiya sun kashe ni. ni kuma ina ganin haka na umarci iro da ya dauke ni ya kaini kauyensu saboda inhar na cigabada zama a garin Azare babu shakka amaryata zata iya samun labarin ban mutu ba sai ta sa a kara zuwa a ce za a kashe ni. sai abokina iro ya amince da batun da na gaya masa. dan haka sai ya bar kasuwancinsa saboda ni muka dawo nan garin kano cikin wannan kauyen da yake gabas da garin nan. Abokina iro ya ban sanarwa akan na sanarwa police don asan matakin da za a dauka haka kuwa aka yi bayan na samu lafiya sosai sai muka koma Azare muka yi report ga "yan sanda, amma da yake kasar nan ta lalace sai amaryartawa ta bawa "yan sanda makudan kudi daga cikin kudadena da nake tarawa. dan haka sai "yan sanda suka ban rashin gaskiya. haka na hakura muka dawo nan kano, bayan wata biyu iro ya kara ban shawara na je na kai kara kotu. sai na ce masa ya bari kawai domin kuwa duk inda muka je mu baza a ban gaskiya ba duk da dukiyata ce kuma ita mata ta ce saboda ba ni da kudi. haka dai ya takura min har na shigar da kara, amma sai aka ban rashin gaskiya a kotun ma saboda amaryata ta tura musu kudade, harma aka ci tara ta naira dubu hamsin. ni kuwa ba ni da ko ficika haka iro abokina ya siyar da abubuwan da yake siyarwa kasuwa a cikin garin Azare ya har hada ya ban kudin na biya. haka na na dawo nan garin kano kauyen su iro na cigaba da zama cikin kunci da damuwa, sai kuma Allah ya jarrabe ni da son mata ta Fatima da kuma "yata Fatima wadanda sun jima da mutuwa, dan haka duk lokacin da na ji an ambaci sunansu sai nayi ta zubar da hawaye ina begensu. haka na kasance a kauyen su iro, har iro yayi aure sannan ya umarce ni nima nayi aure. sai na ce masa ai ni da aure har abada. haka ya ringa ban hakuri a kan nayi aure amma na ce sam ba zan kara aure ba sai dai wani ikon Allah. haka ya hakura da ni muka cigaba da zama. mukan yi shuka duk shekara, duk amfanin da muka samu idan munyi noman idan mun siyar kudin da na samu na kan aikawa "yan uwana a can garin Azare domin kuwa ban manta da su ba. haka na kasance cikin wannan halin har ya zuwa lokacin da muka tsinci Asmeer a cikin jeji kusa da kauyen mu har muka dauke shi sannan muka zo nan da shi. koda baabar hajiya da sauran mutanen da ke wajen suka ji labarin khamal sai suka tausaya masa sosai, baabar fatima sai da ta zubar da hawaye. sai ita ma ta kwashe dukkanin labarin abun da ya faru tun lokacin da ta dauke fatima lokacin da take yarinya har ya zuwa lokacin da take bashi labarin. koda khamal ya ji cewa "yarsa na raye sai ya fashe da kuka sannan ya ce wa baabar fatima ina fatiman take maza hanzarta kai ni wajenta na nemin tubanta. sai baabar fatima ta ji tausayin khamal ainun. sai ta juya ta kira fatima ta ce fatima zo. bayan fatima ta zo sai khamal ya ce yauwa wannan ce zata kai ni wajenta ke nan? sai baabar fatima a goge hawayen da ke zuba daga idanuwanta sannan ta ce ai wannan ita ce "yar taka FATIMA ZAHRA. [9:33AM, 6/16/2015] Asmeer: yana jin cewa an ce masa ai wannan tsaleliyar budurwa da take tsaye a gabansa ita ce fatima sai ya kara fashewa da kuka ya ce ita ce haka ta girma? ikon Allah. sai ya durkusa a gabanta ya na cewa "yata ki ya fe mun dukkanin abubuwan da na miki. sai fatima ta durkusa a gabansa ta ce daina kuka Abbana na yafe maka duk abun da ka min tun daga zuwana duniyar har zuwa yanzu. sai khamal ya kara fashewa da kuka sannan ya mike tsaye yayiwa baabar fatima godiya mai tarin yawa bisa kulawar da ta bawa fatima. Asmeer ne ya kariso wajen cikin sanyin jiki ya zo ya zo gaban khamal ya ce kai hakuri baba ka daina kuka ai komai ya wuce. sai khamal ya ce dole nayi kuka bisa abubuwan da wannan baiwar Allah ta min. sai baabar fatima ta ce ai wannan wanda ke tsaye a gabanka wato Asmeer shi da hajiya sun suka kara bamu kulawa ni da fatima har ya zuwa yanzu. sai khamal juya kan Asmeer ya masa godiya. Haka dai police suka umarci kowa da ke cikin palon da a tafi zuwa police station, haka aka nufi police station bayan kwana biyu aka mika su manaja zuwa kotu har aka yanke musu daurin rai da rai tare da horo mai tsanani har da wannan police din da aka hada baki da shi aka kashe yaran bakin arne bisa kamo shi da aka yi acan lagos. Asmeer kuwa hajiya ya kai asibiti domin sama mata lafiya har ta samu lafiya. bayan ta samu lafiya sai aka bata labarin mahaifin fatima wato khamal haka tayi farin ciki sosai har ta sa ya dawo wajenta ya cigaba da zama a wajensu gaba daya. Bayan wata biyu ne hajiya ta nemin auren fatima a wajen khamal mahaifin fatima sai ya ce ya bawa Asmeer fatima har aka yanke rana kafin zuwan lokacin ne Hajiya da baabar fatima suka hada baki akan su nemi aure khamal gaba dayansu. haka kuwa aka yi suka samu khamal suka yi masa bayani sai ya amince. sai ya zamana lokacin bikin su Asmeer sai aka hada bikinsu da na iyayensu aka yi gaba daya. kai anyi shagali sosai wanda ba a taba yi a garin kano ba. haka aka yi aure aka sha hidima aka watse, "yan uwan khamal da na baabar hajiya sai da suka zo bikin. sai "yan uwan baabar fatima suka nemin tubarta bisa abun da suka mata sai tace bakomai ya wuce ai. Bayan an gaba biki ne komai ya dai dai ta sai hajiya ta mikawa Asmeer duk dukiyar mahaifinsa da dukkanin kadarorinsa daman nasa ne na gado. dan haka sai Asmeer ya bawa khamal mahaifin fatima manaja mai kula da kayayyakin da suke shugowa daga kasashen waje. sai ya zamana Hajiya ta sa Asmeer ya gina babban gida. bayan ya gina sai tace duk "yan uwanta da na "yan uwan Asmeer na wajen mahaifinsa da "yan uwan khamal da na baabar fatima duk su dawo wannan gidan. sai dukkaninsu suka dawo sai hajiya da kanta ta ce to gidan nan su nan shi BIG FAMILY. ****ALHAMDULILLAH**** Godiya ta tabbata ga Allah da ya ba ni ikon kawo muku wannan Labarin. Allah yasa mu amfana da darrusan da ke cikin Labarin. AMEEN

RAYWAR FATMA ZAHRA COMPLETE (dandalin littafan hausa)

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *