Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Saturday, December 5, 2020

HAQQI COMPLETE HAUSA NOVEL

adsense here

HAQQI COMPLETE HAUSA NOVEL

 Compiled by Princess Aysha Muhammad (Humaira) 



[5/17, 15:33] Umar Dalha: ☠HAQQI☠


        ✍🏾mr. melody💥                                       


          🌙april-2017


     

    IT'S PAGE 1⃣-1⃣0⃣ ONLY

                   AND

⇨BEST ON A TRUE LIFE⇦

     

      




    

          Page1⃣&2⃣







*Dedicated to my beloved sisters ummi-aysha & fatima-bintu👩‍👧*







~Actually this what was happened to our elder brother and our friend also, finally he has answered Allah's call already since last two years ago. May your gentle soul rest in perfect peace (muhammad abdullahi) ameeen~






βismillahir rahmanir rahim





Ranar saturday quarter to 11 O'clock morning na

tashi daga ghetto nayi shaye-shaye na fitar

hankali wiwi, madaran suku die, coideen, drugs

kai in takaice muku  zancen duk wani abu da kuka sani

mai gusar da hankali banda giya sai dana sha shi sannan na

kama hanyan gida. Tafiya nake ina malangarine kamar akwalan keke yara su kayi dan-dazo suna min ihu suna cewa “yayi marisa ya sha capsule sha" idanu na a rufe suke kuf! kamar mai bacci saboda shawuwan da nayi, nan take na lalubi duwatsu a kasa jifa kawai na fara yi kota ina kamar zararre har na fasawa malam yusuf limamin unguwar mu kai, yaran duk suka watse kowa sai gudu yake ga sabon mahaukaci.

     Saukan bulalai kawai na fara ji a jiki na any how, manyan unguwar mune suka nad'a min na jaki a bisa abunda na aikata na rashin hankali. A

wurin na fad'i kasa sai bacci ga kwatami da bola

a gefe. Nine ban farka ba sai bayan sallah'n la'asar ba wanda yazo ya tashe ni balle ya jany'e ni daga gefen kwatamin, sai naji duk jiki na yana

min zafi da rad'ad'i ga wani uban yunwan da

nake ji a hankali na lalla6a na tafi gida. Zuciya a dakule na bankad'e kofan gidan na kutsa kai ciki, kasantuwar gidan namu na haya ne duk matan gidan suka shige shashin su da y'ay'an su gudun kada na illata su, kitchen na wuce na shiga

bubbud'e tukwane kamar wanda yayi ajiya amma

ban samu koda k'anzo ba hakan yasa na shiga

kwalawa mahaifiya ta kira a tsawace daso!

Daso!! Tana kyarma ta fito da tsohon cikin ta

haihuwa yau ko gobe, “ina abinci na!?" nan ta fara kame-kame “umh umh yi hakuri muh'du,

wallahi ban zata zaka bukaci abincin bane shi

yasa na baiwa su fatima d'azu" “me! Abincin nawa?,

wallahi karya kike, uban ki ne yake nemowa ko

uba na?" “dan Allah kay...." maganar da ban bari ta karasa ba kenan na wanke ta da mari tas! A

kuncin ta na hagu na sake d'ago ta da wani marin a kuncin ta na dama nan fa na hau yin ball da ita tana kuka “wallahi yau sai kin

yabawa aya zakin ta, sai na kashe ki na kuma

kashe d'an dake cikin ki" wallahi haka nayi ta jibgan mahaifiya ta ko tausayin ta bana ji, nan ta shiga rera kukan neman agaji tana kuka mai cin rai wai ga d'an data haifa nan yana dukan ta instead of ko zagi kada ya jawo mata, wallahi musa ina baku labari duk sanda na tuna abubuwan da na yiwa mamata a rayuwa sai naji kamar na kyastawa kaina wuta ko zan d'an ji sauk'i a cikin zuciya ta, nida aboki na aliyu da ake bamu labarin banda hawaye babu abunda muke yi, gaskiya *HAQQI* ba wasa bane dan wallahi ya zarce tunanin mutum balle aljan, duk wanda ya san muh'd idan ya kalle shi a cikin wannan halin wallahi sai yayi masa kuka, ya kumbura sosai na fitar hankali domin rigan jikin sa sai in an raba shi kashi biyu sannan zan d'au daya a hakan ma zai min yawa, a wannan halin da yake ciki duk da cewa ba wanda yasan gawan fari amma wallahi shi bana tunanin zai wayi gari da rai, duk wanda bai san meke faruwa bama zaiyi tunanin cewa ko yana dauke da wani cuta ne amma wallahi al-hak'i ne kawai ke bin sa. Any where lets back to our normal business, ni kuwa ko a kwalar riga ta balle naji tausayin d'an dake cikin cikin ta sai kace ba ita ta haife ni ba.

   Shovel na dauko na shure ta da kafa ta fad'i kasa na d'aga shovel d'in zan kwad'a mata ta saki kara iya karfin ta hakan yasa ali, hamza

da dauda shigowa cikin gidan a guje suka bankad'e ni

gefe nayi tangal-tangal kamar zan fad'i ali ya hauni da masifa “mahaukacin ina ne kai? Wannan ba mahaifiyar ka

bace Dan uban ka? Ko baka san da ciki a jikin ta bane kayi mata duka haka?" kafin na ankara naji saukan mari on my left cheek tas! Wallahi har sai dana ga star-stars, d'agowa nayi naga hamza ne tsaye a kai na kafin nayi yunk'urin tashi ya kai min a wonderful punch a fuska ta wanda yasa baki da hanci na suka

fashe. 

     Dama hamza ko ransa ba a 6ace yake ba yana cracking sosai during speaking balle a yanzu dana ga ya harzuka sosai zagin ma ya kasa yimin sai bugun da yake ta kai min any how. Dukkanin su

abokai na ne and also my age mate sai dai yadda nake jin tsoron su bana

tsoron wani mahaluki a duniya ban san dalili ba, a cikin su hamza ne kad'ai abokin shaye-shaye na amma ali da dauda basu ta6a shan koda tramol ba balle other drugs masu gusar da hankali. 

   With hamza's cracky voice yace “kai dan

uwar ka wannan ba uwar ka bace? Wani irin

kwaya ka sha yau?" ali da dauda suna can wurin

mamata data ke rera kuka suna bata hakuri daga karshe suka tattara ta izuwa dak'i. Duk wannan chakwakiyar da muke yi ba wanda ya shigo haka zalika ba matar data fito a cikin gidan. Kamani su kayi suka min d'aurin sweet wato sama d'auri k'asa d'auri da igiyan shany'a sannan su kayi waje dani.

     Garden suka kai ni inda babu wanda zaiji sautin kuka na balle ya kawo min agaji. As always kamar yadda nasan dauda da hamza basa rabuwa da bulalan cable mai baki goma a jikin su, with my big surprise gani nayi sun d'aga riga gami ciro bulalan cabels d'in a kunkumin su, kowa yana rik'e da nasa. Hamza da crackcy voice nasa yace “yau zaka ci uban ka, in

shaye-shaye ne zaka nuna min ne? yaushe Ka fara shan kwaya ne harda zaka je ka sha wani drugs wanda ko gajiya bazai iya cire min ba zaka zo ka yiwa mamar ka duka?" ihu

nake yi tsakani da Allah ina basu hak'uri can naga ali ya zame jikin sa ya bar wurin ashe dai shima bulalan yaje tsinkowa, kawai ganin sa nayi ya fito da santalelen bulalan k'aya yana zuge gany'any'akin dake jikin bulalan. Ai kuwa volume na ihun nawa ya dad'u kamar wanda yaga mala'ikan mutuwa saboda yadda naga sun had'e rai suna wani zazzaro min na mujiya nasan dakuwa zanyi na fitar hankali wanda idan aka kaini asibiti sai likitoci sun tambaye ni da damisa nayi fad'a koda zaki.

  Without noticing of anything naji sauk'an duka tun ina ihu har murya na ya dashe sai sautin saukan bulalai kawai ke tashi a wurin, sai da nayi laushi sosai

sannan suka kyale ni, nafi 2 hours ban san a ina nake ba farkawa kawai nayi na ganni kwance a kan gadon asibiti da drip a hannu na wai ashe har sun kawoni gida mahaifina na yayi ta masifa daga karshe ya kirawo y'an Qato da gora a kayi gaba dasu a kan cewa sai time d'in dana farka zasu bada bailing. wallahi na daku a wannan ranan jiki na ya farfashe sosai ko ta ina kwarzanin bulalan k'ayan ali ne sai kuma fashewan da jiki na yayi wannan kuma na bulalan cabel nasu hamza ne.

       *~*~*~*~*~*

 The following day, 8㏂ mamata ce da kanta taje tayi bailing d'in su hamza daga office na y'an qato da gora suka dawo gida. Ni kuwa bayan likita yazo ya dubani yayi prescribing min wasu medicines d'in da ya aika wata nurse ta d'ebo masa a dispensary sannan ya had'a mana da takaddar sallamar mu tare da yiwa baba na gargad'in cewa kada a sake bari na, na sha kwaya saboda kwayoyin da nake sha sunfi karfin jini na baba na yace “toh zamu kiyaye insha Allahu doctor". bayan mun dawo gida kannena aisha da fatima sun dawo daga tallan awara baban mu yace “ke aisha?" “na'am baba" ta amsa mai “dauko mana tabarma da sauri" bayan ta dauk'o ya umarce ta data shimfid'a min tabarman. Bararrajewa nayi a kan tabarman, baban mu ya shiga kwalawa mamar mu kira “daso?! Daso!?, wai baza ki fito bane?" “Gani nan zuwa" ta fito tana mai cizon le6e da turo cikin ta “yanzu ke maryam ashe baki da mutunci? Baki da hankali? D'an nawa tilo kika zuba ido abokan sa su kayi mai dukan tsiya eyyeh?" “Haba malam? Kai kenan baza ka daina d'aurewa karya gindi ba? yaro yana neman halaka ni y'an albarka suka kwace ni a hannun sa da kyar amma kake wannan furucin?" Ta kare maganar cikin sautin kuka, haushin ta kawai na fara ji take na fara kwarara mata ashar baba na yana ji amma haka ya kyale ni na rinka zagin mahaifiya ta wacce a yanzu ita take kula dani day and night duk da cewa abubuwan da nayi mata a rayuwa are unforgettable and unforgivable ne amma a haka take bani kulawa na musamman, ban ta6a sanin tana sona ba sai dana fad'a cikin wannan bala'in mai tsanani, tunda mahaifiya ta ta haife ni ban ta6a sata farin ciki ba kullum sai nayi mata abunda za tayi kuka amma bata ta6a bud'e bakin ta tace min muh'd Allah ya wadai da kai ba. Musa, Aliyu wallahi na zalinci kaina, ku duba kuga yadda na dawo? Duk wanda ya kalle ni sau d'aya baya marmarin ya sake kallo na amma ga uwata nan wacce na raina wacce na tsana ba tare da tamin komai ba ita take caring d'ina. Nayi kashi, fitsari ta wanke, nayi amai ta goge, idan kayana sunyi daud'a ta wanke min su ta kuma yimin wanka, sai kuma ya fashe da kuka mai tsuma zuciya abun tausayi da shi. Yana shesshek'a yace “yanzu dare yayi musa, quarter to 10㏘ ya kamata kuje gida ku huta zuwa gobe insha Allahu sai mu daura daga inda muka tsaya, hawaye ne kawai ke forming on our both left and right cheecks nida aliyu nace “Allah ya kaimu da rai da kuma lafiya, sai da safe" yace ameen Allah ya nuna mana, ko uffan aliyu ya kasa cewa sai hawayen da yake ta zubarwa muka fice  daga dak'in. Mahaifiyar sa ce zaune a kofar dak'in bisa tabarma muna wiping off our tears with hanky nace “toh mama mu zamu wuce sai da safe" “toh musa ku huta gajiya ko? mun gode! Mun gode!! Allah ya saka da alkhairi ya kuma bar zumunci" da kyar aliyu ya iya bud'e baki yace “ameen" “aliyu ka gaida min maman ku sosai da gajiya and you also musa" da “toh" muka amsa mata sannan muka fice...



😊мr. мεισdγ🍉



[5/17, 15:33] Umar Dalha: *LITTAFI* HAQQI☠






    


       ✍🏾mr. melody💥








          🌙april-2017



   





            page3⃣&4⃣







*Dedicated to my beloved sisters ummi-aysha & fatima-bintu👩‍👧*





Yau take sunday ban fita wurin aiki na ba kasantuwar ina hutu, bayan nayi wanka around 9㏂ na kira aliyu a waya not long enough sai gashi yazo muka wuce al-arfat

shopping complex muka d'anyi sayayyan drinks daga ciki akwai maltina, bitter lemon, exotic, fresh milk da sauran su, a k'alla dai munyi spending kud'i 1k sannan muka wuce gidan su muh'd. Kamar kullum yau ma mahaifiyar sace zaune a gefen sa da kanta take feeding d'in sa break fast da soyayyan doya mai kwai sai black tea. “yau Kune a gidan namu da safe haka?" “hmm eh wallahi mama, ina kwana?" Muka fad'a tare da aliyu yayin da muka durkushe har k'asa “lafiya qalau y'ay'an nan, ya su maman ku da sauran yaran?" “kowa lafiya qalau wallahi mama, ya mai jiki?" “toh ga mai jiki dai, sai addu'ah" “Allah sarki, Toh Allah ya bashi lafiya ya kuma sa kaffara ne" da “ameen" ta amsa mana sannan ta fice ta bamu wuri muka zauna gami da ajiye shopping d'in da muka yo masa a gefen sa. Kallon sa kawai na tsaya yi saboda naga kumburin nasa ya dad'u ba kamar na jiya ba, “sannu muh'd, Allah ya baka lafiya" abunda aliyu ya iya fad'a kenan “ameen aliyu, ina gajiya musa?" “ba gajiya wallahi, kana cin abinci muka katse

ka ko?" fake smile yayi “no karku damu dama i'm

platefull kawai dai ta matsa min dana ci ne that's all" ajiyar zuciya aliyu yayi sannan yace “Allah ya kyautata

karshen mu" mu duka muka ce “ameeen" daga nan dak'in ya dauk'i shiru na wasu y'an dak'ik'u kamar ba halittu a cikin sa duk munyi zugum, chan! aliyu ya nisa sannan yace “anya muh'd zaka iya cigaba da bamu labarin nan kuwa?" “why not?, insha Allahu zan iya don't bother yourself" "toh shikenan muna sauraron ka" na fad'i hakane yayin da nake gyara zama dan

sauraron labarin da kyau.

    bayan na fara samun sauk'i daga dukan da su

hamza suka min na d'an fara fita waje dan shan iska, as you know already mahaifin mu jobless ne bashi da aikin fari balle na bak'i, yau shine wannan

gobe shine wancan da ky'ar yake iya samo mana na abinci balle y'an kud'ad'en da zamu biyawa

kawunan mu bukatu dasu, duk da rashin da muke fama da shi na talauci amma a haka idan maitana ya tashi wato kwad'ayin shaye-shaye na idan ya motsa tisa shi nake a gaba har sai ya bani kud'i, wani lokacin ya bani 500 wani lokaci kuma 200 saboda ni kad'ai ne namiji babba a gidan mu shi yasa bana tambayan abu na rasa kamar yadda nima bana tambayar abunda nasan yafi karfin gidan mu. Ta sanadiyar wannan gatan da yake nuna min ne yasa na 6aci dan har yau ban iya wani aikin hannu ba infact ban ta6a yin wata sana'a ba kullum mahaifina ne ke bani kudi, shi kuwa idan na tambaye shi kud'in bani kawai yake yi baya tambayata me zanyi dasu ni kuwa sai naje can ghetto na kashe mana kud'in tas! a kan kayan maye tare da abokai na, na banza.

   Wata rana mahaifin mu ya dawo daga gona, gonar

ma ba tasa bane daukan sa haya aka yi wato

barema, ko gida ban kyale sa ya shiga ba na tare

shi a bakin kofar gidan ba tare dana kar6i icen da ya d'auko ba balle nace masa sannu da zuwa. Kai

tsaye nace “baba bani da kud'i fah kuma ina jin

yunwa" “toh baka ci abinci bane ko basu girka bane?"

fuska na 6ata “ni in za'a bani a bani ba wai a tisa ni a gaba da tambayoyi ba, in kuwa baza a bani bane let me know shine kawai ehe!" sai daya d'an 6ata lokaci yana kallo na finally ya d'an karkace ya zaro 1k yace “toh gashi kaje ka kawo min 800 yanzu" kar6an kud'in kawai nayi ba tare da nayi godiya a gare shi ba sai ma y'an kumbure-kumburen dana keyi, reason nayin hakan kuwa shine 200 ya min kad'an. Ghetto na wuce wallahi sai dana ga bayan 200 d'in nan a kan kayan maye sannan na dawo gida.

    Rannan mahaifiya ta tana toya awara wa kanne na a kitchen suna kaiwa godiya private school na diro mata ba sallama shiru tayi min gudan kada tayi magana nayi mata wani abun, matsami na

dauk'a na kwashi awara a cikin man tuyan na zuba a plate sannan na barbad'a yaji a kai. Duk abubuwan dana keyi bina kawai take da ido “wai ya da kallo hakane? Ko sai na bad'e idanun da barkono ne sannan zaki daina kallo na?" nayi maganan ina mai zare mata ido kai kace da y'ata nake maganar bada MAHAIFIYA TA ba. “yi hakuri ka jeka, babu komai ai duniya ce" doguwar tsaki naja sannan nace “lahira ce ba duniya ba iskanci kawai" ina kaiwa nan na shige cikin dakin ta na zube a kan single couch nata na d'aura plate na awaran bisa cinya ta sannan na hau awaran da chi like there's no tomorrow. Bayan na cinye awaran sai kuma naji kwad'ayin shaye-shaye na ya motsa and my pocket was dried nan fa na shiga chaje mata dak'i da kwanuka amma ban samu koda kwandala d'aya ba, zuciya a dak'ule zan fita kenan sai kuma nayi step backward kasantuwar mahaifiyar tawa uwar adashe ce sai na karasa kan gadon ta na d'aga pillow, wani jaka na gani irin wanda ake daurawa a k'ugu mai d'an girma haka, nan fa zuciya ta tayi haske ban tsaya wata-wata ba na bud'e jakan, dubu-dubu, dari biyar-biyar sai y'an dari bib-biyu na gani a ciki wanda ni kaina ban san ko nawa bane, tattara su nayi kaf! Zan fita dasu kenan sai kuma naji tausayin ta ya kamani “yanzu idan na tafi da kud'ad'en nan ai zata iya rasa rayuwar

ta ko?" Tambayar da na yiwa kaina kenan, take imani ya ziyarci ruhi na, 200 kachal! na dauka a cikin kud'in na mayar mata da sauran cikin jakan na tura shi karkashin pillow'n kamar yadda yake as before wanda baza tayi tunanin wani ya ta6a mata kud'i ba. 

    Ghetto na wuce nayi ta shaye-shaye wanda har sai da zama ya gagara tsayuwa ta gagara, a ghetton ma na kwana tsabakin yadda na shayu na gama ficewa a hayyaci na gaba d'aya. 

 Hmm muh'd yayi murmushin takaici sannan yace “wannan fah ina

baku labarin aika-aikan dana keyi a cikin gida ne

dan wallahi hatsabibanci na ya wuce nan." Wannan karon ni ko aliyu ba wanda yayi hawaye a cikin mu sai sauraron sa kawai da muke yi, aliyu yace “toh muna sauraron ka muh'd, ka bamu labarin kato6aran

daka tafka a waje amma kafin nan ga wannan ka d'an sha" yayi maganar ne yayin da ya bud'e ledan drinks d'in da muka taho masa da shi ya d'auko maltinan gwan-gwani ya bud'e sannan ya mik'a masa, kad'an ya sha ya ajiye sauran.

    Sanin kanku ne musa, a daa lokacin ina ji da kaina iskanci babu wanda bana yi, fannin mugunta da cin zali kuma kowa ya sallama min dan ba'a barni a baya ba. Wata rana da yamma muna zaune chamber ni, ali, hamza, dauda, abdullahi da kuma yusuf muna hira sai ga hassan mamar sa ta aike sa shagon abbo siyan flower, yazo wucewa kenan na kira sa “kai hassan zo nan" ya waiwayo ya kalle ni ba tare da yana zuwa ba, “wai baza ka zo bane?" na fad'a a tsawace still yak'i zuwa na tashi a fusace nayi kansa “kai dan uwarka ba kiran ka nake yi ba?" kuka ciki-ciki ya fara yi na zabga masa tafi yasa ihu “dan uwarka kayi kukan da tushe, in uban ka ya kira mu bama zuwa ne?" Da wannan na kyale shi yayi kwana abin sa, sai da yayi nisa kad'an yayi min dak'uwa yana cewa “kaci uwar shege tsinanne munafiki mugu azzalimi kawai" “ni ka zaga?" na fad'a da d'an ihu gami da pointing na kaina “eh kai d'in mugu kawai, kuma wallahi Allah ya isa na" “ai kuwa yaro ka zama nama dan wallahi idan na kama ka sai naci uwar ka" a haka fa na hana yaro zuwa aike, da isar sa gida bai jima ba sai ga mamar sa ta fito dama bata da hakuri idan ka ta6a mata y'ay'a, daru mu kayi da ita sosai finally abun ya bani haushi nace da ita “sai dai in bazai na fita waje ba, amma wallahi muddin na rik'e shi sai naci uwar sa" “au! Rashin kunyar taka har ya kai kace zaki ci uwar d'ana? Lallai yaron nan mahaukaci ne kai" Da kyar su hamza suka bata hakuri ta amince, dan cewa tayi sai ta kira min police su tafi dani, duk da cewa ina tsoron zuwa bayan canter amma sam! ban nuna mata a fili ba sai dad'a kurari nake.

   Haka dai rayuwa ya cigaba da tafiya kullum cikin rikici nake, na daki d'an wannan na daki d'an wancan har y'an unguwa suka kai report wa babana cewa na fita hanyar y'ay'an su ko kuma su dauk'i matakin daya dace, ni dai bana kwa6uwa dan kuwa sai dai ayi ta min surutu amma duk a banza na riga na zama fitinanne na kin karewa idan naje nayo shaye-shaye na dawo gida duk wanda na samu mahaifiya ta ko kanne na sai na jibge su iya son raina baban mu baya cewa komai sai dai idan su hamza ne suka min duka a bisa dukan mamata ko kanne na da nayi. Ina mai tabbatar muku cewa mahaidiya ta, ta kamu da ciwon hawan jini nine ta sanadiya ta. A nan ya fashe mana da kuka yana zubar da hawaye zafafa, in between crying yace “dan Allah aliyu ka kira min *MAHAIFIYA TA* na sake neman gafarar ta" wallahi da wannan furucin nasa ya karya min zuciya ban san lokacin da hawaye suka fara rolling on my both cheeks ba. Kamar yadda ya bukaci aliyu daya kira mai mamar sa not long enough suka shigo tare gaba d'aya hankalin ta ya gama tashi a zaton ta jikin nasa ne ya tashi, a gaban ta muh'd ya zube on his knee gami da duk'ar da kansa k'asa yace “dan Allah dan annabi mama ki yafe min, ki gafarce ni ba dan hali na ba, ban kyautata wa kaina ba ko kad'an, wallahi kaicho na!!" ya kare maganar da kuka mai tsuma zuciya a hankali ya sulale k'asa ya kama kafafun ta yana neman tuba sai kukan da yake yi mai sauti.



😊мr. мεισdγ🍉



[5/17, 15:33] Umar Dalha: *LITTAFI* HAQQI☠

        







     ✍🏾mr. melody💥

       






          🌙april-2017                       

              


           



           Page5⃣&6⃣






*dedicated to my beloved sisters ummi-aysha & fatimah-bintu👩‍👧*





Tausayin sa ya dad'a lullu6e mata zuciya bata ma san lokacin data fara zubda hawaye ba. 

Duk'ar da kaina nayi k'asa wasu zafafan hawaye nake tsiyayarwa na d'an ta6a aliyu nufi na ya tashi mu tafi amma sai ya gyad'a min kai alamun a'a ba yanzu ba, ni kuwa zuciya ta baza ta iya jure ganin muh'd da mahaifiyar suna kuka ba, hakan yasa na tashi zan fita aliyu ya rik'o min hannu ba yadda na iya dole tasa na zauna.

   “Muh'd na yafe maka duniya da lakhira, Allah ya baka lafiya ya kuma yima albarka" tayi maganar cikin kuka gami da d'ago sa daga durkushen da yake ta rungume shi shima yayi hugging nata back yana kuka tana bug-buga bayan sa yana cewa “nagode mama Allah ya saka miki da gidan Aljannah, lallai kin cika uwa ta gari" sun d'au lokaci mai tsawo a rungume da juna finally tayi breaking hug d'in a hankali. “mama?" Yayi exclaiming d'in sunan ta da sark'ak'iyar muryar sa “na'am muh'd?" “mama Ina su aisha, fatima da aunty?" Hawayen dake rolling on her both cheeks ne tasa hannu tayi wiping off sannan tace “sun tafi talla, me kake so suyi ma?" “Ba abunda nake so suyi min face gafara, domin na zalince su a rayuwa" ya kare maganar da kuka. Lallai rayuwar muhammad tana k'unshe da darussa bila adadin, wanda mu matasa ya kamata muyi duba ga yadda rayuwar muhammad take a daa can baya, shan kwaya bashi da wani fa'ida kuma ba abunda baya haifarwa, yanzu wani abu da yake damun mu, mu matasa shine wai idan kai baka shan drugs, cigarrete, wiwi, oris da shi-sha (pot) muddin dai baka shan d'aya daga cikin wad'annan haramtattun ababen wai kai baka cika gaye ba, a'uzubillahi, toh kada Allah yasa na cika gayen in dai sai nayi shaye-shaye ne. Wato wani abu d'aya da har yanzu mutane basu fahimta ba shine, turawa sun k'irk'iro shi-sha ne ba dan komai ba sai dan su lalata mana tarbiya wanda iyayen mu suka 6ata shekara da shekaru suna bamu ita. Da farko abunda za muyi la'akari da shi a nan shine: shi-sha da oris duk kamshi d'aya ne dasu sai dai shi oris kamar taba yake a nannad'e, karfa ku manta shi-sha tsani ne wanda mutum zai bi a sauwak'e ya fara shan taba wiwi da sauran su ba tare daya sani ba, kullum ka saba shan shi-sha kana sayan flavor 350 ranar da baka da kud'in sayan flavor'n kuma kana kwad'ayin shan shi-sha cewa za kayi “ba gara naje na saya oris naira goma ba na sha tunda duk kamshi d'aya ne dasu" toh daga ranar da tunanin haka ya fad'owa mutum a rai wallahi tasa ta kare domin shaye-shaye zai fara gadan-gadan kuma dan Allah dear readers ku duba ku gani 80% cikin 100% na mashayan yanzu matasa ne, 70% cikin 100% kuma daga shi-sha suka fara shaye-shaye har suka fara shan wasu kwayoyin, dama shi-sha foundation ne na koyan shaye-shaye wanda turawa suka kafa dan lalata tarbiyan y'ay'an musulmai, yanzu ma abun harta 6aci akwai turare mai kamshin flavor'n shi-sha wai (straw-berry) har mutane suna saya su shafa a jikin su dan rashin hankali, yo! Baka sha amma idan ka had'u da wanda bai san cewa turare bane shikenan kimar ka ta zube a idanun sa, kai bada girki ba amma da warin hayak'i. Allah ka kare mana imanin mu ameen ka kuma tsare mu da muggan abokai domin masu iya magana suna cewa zama da mad'aukin kanwa shike kawo farin kai. Masu sha Allah ya shirye su mu kuma da bama sha Allah ya dad'a tsare mu ameen thummah ameen.

    Da kyar na samu nayi convicing na aliyu ya tashi muka tafi gida da sharad'in cewa zamu dawo by 8pm dan jin karshen labarin kasantuwar yau babu zuwa majalis. Haka kuwa aka yi 8pm bayan munci abinci muka wuce gidan. Kai tsaye muka zarce dak'in nasa wannan karon k'anwar sa fatima ce ke gefen sa a zaune tana taya shi hira. Cikin girmamawa ta gaida mu, muka amsa sannan ta tashi ta fice muka zauna. 

   Da fara'a kwance a fuskar sa yace “Sannun ku da zuwa" “yauwa, ya kaji da jikin naka kuma?" a cewar aliyu “hmmm" kawai yayi ba tare da amsa ba “amma muh'd baza ku koma asibitin nan ba kuwa?" Na fad'i hakan ne yayin da nake kare mai kallo dan wallahi babu alamun sauki a tattare da shi saima abunda ya karu. “eh toh abunda yake kaimu asibitin dama magungunan cin abinci ne da kuma irin abincin da doctor yace ina ciki" “haa'ah, kamar ya? Dama basa duba jikin naka ne duk zuwan ku asibitin?" aliyu yayi maganar da mamaki “eh dama tun kafin jikin nawa yayi tsanani likitan ya shaidawa baban mu cewa ciwo na bana asibiti bane kamar yadda binciken su ya nuna bana d'auke da wata cuta daya sa nake wannan kumburin" ajiyar zuciya nayi sannan nace “kun gwada na gargajiya ne?" Ruwan dake gefen sa a cup ne ya d'aga ya d'an kur6a kad'an ya ajiye ya nisa sannan yace “har gombe an kaini amma bamu dace ba, nifa ina ji a jiki na bazan tashi ba" da sauri nace “subhanallahi, bai kamata ka furta wannan kalmar ba, sai kace ba musulmi ba? ka tuna fa cewa ba abunda ya gagari Allah, Allah gagarau ne saboda haka ka cigaba da addu'a muma cikin yima addu'ar muke a kullum kuma insha Allahu zaka samu lafiya" “toh Allah yasa, nagode Allah ya saka da alkhairi ya bar zumunci" nida abokina aliyu muka masa da ameen. “Toh aliyu ne dama ya matsa min akan lallai-lallai muzo ka karasa mana labarin, zaiyu ka karasa mana yau ko kuwa mu hakura sai gobe?" Lumshe idanun sa yayi a hankali kamar mai jin baci yace "gaskya da zaku hakura sai goben da yafi, saboda ina jin kaina yana sarawa ga kuma baccin da nake ji tun dana gabatar da sallah'n magharib" “kash! Subhanallahi Allah ya yaye, ka sha magani kuwa?" aliyu ya tambaye shi “a'a, ban sha ba amma da zarar na samu nayi bacci zan tashi babu ciwon kan" “toh Allah ya baka lafiya, mu zamu wuce gida sai goben in Allah ya kaimu" na fad'i hakanne yayin da muke mik'ewa tare da aliyu “Allah ya kaimu da rai da kuma lafiya, nagode! Nagode!! Allah ya saka da alkhairi ya kuma bar zumunci" da ameen thummah ameen muka amsa masa sannan muka fice bayan munyi sallama da mahajfiyar sa.



😊mr. melody🍉



[5/17, 15:33] Umar Dalha: *LITTAFI* ☠HAQQI☠






   



       ✍🏾mr. melody💥









          🌙April-2017








           Page7⃣&8⃣








*dedicated to my beloved sisters ummi-aysha & fatimah-bintu👩‍👧*





Yau take monday muna da general exam na english paper 1-3 Tun 9:30am sai 4:30pm muka kammala. Bayan mun dawo gida so exhausted tare muka ci abinci da aliyu bayan nan ya wuce gida yin wanka nima na fad'a a family bathroom na gidan mu dan watsa ruwa.

   30 minutes after sai ga shi ya taho sanye cikin kananan kaya white t-shirt ne mai style da y'ay'an beads da ¾ amry trouser ni kuwa jallabiyar makkah na zurmud'a sannan muka wuce gidan su muh'd dan jin karashin labarin nan nasa. Kai tsaye muka fad'a cikin gidan da sallamar mu matan gidan suka amsa muka gaisa dasu sama-sama sannan muka shige cikin dak'in a inda muka tarar da mamar sa tana bashi abinci a baki.

   “Ina yini mama?" muka fad'a tare da aliyu yayin da muke kokarin zuwa kasa “lafiya qalau, sannun ku da zuwa" “yauwa mama, ya mai jikin?" Ajiyar zuciya tayi gami da cewa “wallahi jikin nasa ba wani alamun sauki, jiya iyau koma ince sai dad'uwa yake" na d'ago idanu na, na zuba su kan muh'd wanda tun shigowar mu ya jingine a jikin bango idanun sa a lumshe suke sunyi kanana mini-mini dasu tsabakin kumburin da yayi har za kayi tunanin cewa idanun nasa basa bud'ewa ne. “Allah ya sauwake" cewar aliyu “ameen ya Allah, throughout yau baku zo wurin d'an uwan naku ba sai yanzu, lafiya dai ko?" Murmushin yak'e kawai nayi nace “munje zana jarabawa ne wallahi shi yasa bamu zo ba" “toh Allah ya baku sa'a yasa ku fito da flying colour" da ameen muka bata amsa sannan ta fice. Duk muka yi shiru ba wanda yace koda uffan aliyu ya duk'ar da kansa k'asa kamar me nazarin wani abu, kwallafa idanu na nayi a kan muh'd ina kallon shi cike da tausayawa shi kuwa har yanzu idanun sa a lumshe suke wasu siraran hawaye na gani sun gangaro masa a hankali ya fara yin kuka mara sauti tausayin sa daya min yawa yasa na kasa appeasing d'in sa kamar yadda aliyu ma ya kasa. Yayi kuka mai isar sa ba wanda ya lallashe sa a cikin mu saboda kukan nadama ya keyi bai kamata mu lallashe sa ba, kukan da yayi zai sa ya d'anji sauqi koda kad'an ne a cikin zuciyar sa. Cikin rawar murya yace “sannun ku da zuwa" aliyu ne ya amsa mai da “yauwa" shi d'in ma cikin shesshek'an kuka ne, ya d'aura da cewa “sannu muh'd, Allah yaye ma wannan musiba" kai yake kad'awa a hankali ga kuma hawayen da suke rolling on his cheek “musa baza kayi min magana bane?" Cike da tausayawa na matsa kusa da shi nasa hannu na share masa hawayen da suke sauka kan kumatun sa nace “yi hakuri, sannu kaji? Allah ya baka lafiya ya kuma sa kaffara ne" kukan da nake matsewa ne ya kwace min, gefe na koma na zauna ina matsar kwalla, sai da duk muka saita kawunan mu sannan muh'd ya sauke sassanyar ajiyar zuciya ya kalle ni ya kalli aliyu yace “mu d'aura daga inda muka tsaya jiya ko?" da sauri aliyu ya gyada masa kai gami da cewa “eh". 

    Muh'd ya sauke sassanyar ajiyar zuciya a karo na biyu gami da gyara jinginuwan sa a jikin bangon ya fara da cewa “as usually dama bani da wani aiki sai dai naje ghetto nayi shaye-shaye sai nayi d'ub nake shigowa cikin unguwa duk yaron dana had'u da shi dukan sa nake tamkar aiko ni aka yi daga sama jama'ar unguwa su kayi ta min magana amma kota kawunan su bana bi sai ma ashar d'in da nake ta faman kwararo musu, baban su usaini ne yazo ya sameni ina langa6e a jikin bango sai wani lumshe ido nake saboda yadda na shawu over, yazo ya sameni ne akan na lakad'awa inusa duka kanin usaini har sai da na fasa masa baki “kai muh'du yanzu abunda kayi ya dace kenan?" Cikin yanayi na shawuwa na kalle shi da ido d'aya nace “daga yau kada ka sake kira na da muh'du, kana ji ko?" Duk da cewa a shaye nake amma da sane na nake fad'in hakan, “yo! Ai sai kaje ka fad'awa uban ka wanda ya rad'a ma sunan kace baka so, ina mai gargad'an ka daka fita a idona na rufe dan wallahi zan sa a daure min kai a garin nan" kallo tara saura quarter nayi masa sannan na tsartar da yawu nace “sunana john daga yau in kuma ka sake kira na da muh'du zaka gane cewa shayi ruwa ne, dan wallahi sai y'ay'an ka sun kasa shaida ka balle matar ka" ya tafa hannun sa yace “innalillahi wa'innaillaihir raju'un!, yanzu kai haukan naka har ya kai kace kai sunan ka john? sunan kafiri?" Tsaki naja na bar wurin sai wani layi nake sai kace mahaukacin jaki, shi kuwa bina kawai yayi da ido baki a wangale. Haka dai a dolen-dole na koma arne in ka kira ni da muh'd na kwararo ma ashar in kuwa john kace sai mu zauna lafiya. Wallahi har yau wasu da john suke kira na wasu kuma da shi suka sanni abun yana bani haushi matuk'a amma ba yadda na iya saboda *NI NAIWA KAINA*. A nan ya fashe mana da kuka yana cizon le6en sa dan takaici, in between crying yace “wallahi shaye-shaye ba abu bane ma kyau, da ban fara shaye-shaye ba, da duk ban tafka rashin hankali dana tafka a duk tsawon rayuwata ba. Nothing is hurting me more and more! like the way that i treated my only mumy harsly like this" kukan nasa ya fad'ad'a Ya sake cewa “peoples are saying what you sow is what you reap either good or bad, yes of course they are right because i have now started reaping all bad things that i have been sowed since" yana kaiwa nan a zancen sa ya duk'ar da kansa kasa yana wani irin kuka mai karya zuciya yana maimaita astagfirullah! Wa'atubu ilaihi Astagfirullah! wa'atubu ilaihi!!...



Kai jama'a Allah yasa mu dace, matasa dan Allah mu kiyaye shaye-shaye bashi da wani anfani sai ma cutar da lafiyan d'an adam da yake yi. Likitoci sun bayyana cewa shaye-shayen cigarrete, wiwi ko shi-sha yana ru6ar da huhun d'an adam, yana ta6a lafiyar kwakwalwa sai kaga mutum shi kad'ai yana ta surutai, yana jawo cutar daji wato cancer, uwa uba kuma yana zubarwa da mutum mutuncin sa a idanun al ummah. Su kansu masu company'n me suka ce? Cewa su kayi (the federal of ministry of health warns that smokers are liable to die young) abunda suka rubuta a jikin kwalin kenan, abu mai kyau ba sai an fad'a maka cewa wannan abun mai kyau bane kai kanka ka sani, ai ido ba'a nuna masa bacci. Sanadin shaye-shayen nan kwanaki a damaturu na samu labarin cewa wani matashi da bai wuce 22 years ba yaje sha kwaya ya dawo gida ya hallaka mahaifan sa duka biyu har hoton sa na gani, dan Allah me anfanin shaye-shaye ya y'an uwana matasa? bakwa bukatan karin haske ku kanku kun karanta labarin kunji me late muhammed abdullahi ya aikata, kar kuyi zaton ko fictitious story ne wallahi it is true. Bani da ta cewa sai dai nace Allah ya jikan sa da rahama yasa tuban sa kar6a66iya ce mu kuma Allah ya kyautata karshen mu ameen thummah ameen.



😊mr. melody


🍉

[5/17, 15:33] Umar Dalha: ☠HAQQI☠





  




        🌙April-2017


.





       ✍🏾mr. melody💥







         Page9⃣&1⃣0⃣






*```this page is dedicated to you my besty <aliyu garba-ALi baii> ana mugun tare wallahi nawan```*





Bayan yayi ta istigfari daga bisani yayi murmushin yak'e sannan yace “a rana mai kamar ta yau monday itace babban ranar nadama a gare ni, kuma babban ranar farin ciki a gare ni domin ta sanadiyar wannan ranar na nema gafarar *MAHAHAIFIYA TA* kuma ta yafe min masha Allah, my only mum may Allah (s.w.a) reward you jannatul fiddaus ameen thummah ameen i really so much love my momma you are one in a billions".


    “I thought ranar da muke zaune a chamber'n kofar gidan mu tare daku muke zaune ko?" zallan Kai kawai muka gyad'a mai alamun a'a ”no bad yau za kuji komai" ya fad'i hakan ne yayin daya d'an kora ruwan faro saboda an hana shi shan ruwan randa kona fan-fo sai swam ko faro.


    WAto ranar misalin karfe 8 bayan sallah'r i'sha, kwance muke a chamber muna shan iska kasantuwar zafi ake sosai, wani almjiri ne wanda da kyar ya kai 13 years ya shige cikin gidan mu yayi ta bara yak'i fita ni kuwa abun ya bani haushi sai na harzuka na shiga cikin gidan na fito dashi na wanke shi da gigitacciyar mari take ya fad'i kasa sumamme y'an uwan nasa da suka ga haka sai suka kira manyan su suka tafi dashi makarantar su.


    Wannan yaron dana mara ba-barbare ne (kanuri) Haka y'an makarantar nasu ma duk kanurai ne harda malaman. Haka dai na kwana lafiya a wannan ranar kamar maye yaci shirwa. Safiya nayi guraren karfe goma zuwa sha-d'aya da y'an kai, zaune muke a chamber muna break fast da fara da mai (garau-garau) wanda mamar su shukura take yi na sayar wa.


    Garadan makarantar su almajirin dana mara daren jiyan ne nayi tozali dasu sunyo gayya kwannen su yana rik'e da allon sa sun nufo kan mu, ganin hakan yasa na tuno da abunda na aikata jiya. Gida na shiga na biya ta kofar baya na gan-gara kasan kwari na gudu.


    Da zuwan su chamber'n suka tambayi abokan yaron dana mara d'in cewa “a cikin wad'annan wanne ne ya mari baana?" Yaran duk suka kid'ime suka kasa tunano fuskata sai suka nuna modu, modu na ganin an nufo kan sa da saran allo yasa ihu yana cewa “wallahi tallahi bani bane wanda ya mare sa ya gan-gara k'asan kwari ya gudu".


    Wani babba daga cikin su yace “ya gudu?, toh wallahi baza mu kyale shi ba sai mun d'auki fansar d'an uwan mu" jama'ar unguwa su kayi chaa! A gun kowa naso yaji meya faru. Many'an unguwa suka karaso jama'a suka bub-bud'a musu suka shigo inda garadan nan suke.


   “Meke faruwa ne aaramma?" Baban su ishaq ne ya tambayi jagoran nasu, yana huci yace “alan-guro wani yaro a gidan nan ya mari d'an uwan mu daren jiya dan yazo yayi bara, yanzu a haka yaron yana can a kwance ba lafiya toh wallahi tunda ya gudu sai mun d'auki fansa" yana kai aya a zancen sa yace “kai kuzo mu tafi" baban su ishaq da sauran jama'a su kayi ta basu haquri amma ina sun kafe a kan magana d'aya sai sun d'auki fansa.


    Nine ban dawo gida ba sai bayan sallah'r magharib. A nan ne aka labarta min komai, a cikin daren baban mu ya nemo min kud'in motan zuwa maiduguri akan naje can nayi zama na a gun k'anin sa after magana ya lafa sai na dawo gida saboda idan na tsaya naki tafiya zasu iya dawowa ako da yaushe kuma babu shakka zasu d'au fansar su.


    Dama banyi kwana biyu da yin d'aurayan kayaki na ba, wad'anda suke da datti baza su wuce set biyu bane a ciki, da asuba na kin-kimi jaka ta na wuce tashar motoci terminors.


    A maiduguri nayi spending 2 months bayan komai ya lafa harma na manta da rikicin daya koro ni daga garin *biu* jiki na ya fara kumburi da naga cewa abun baya yin sauk'i sai na tattara na dawo gida gudun kada jikin nawa yayi worst bana gaban mahaifana.


    Abu kamar wasa Duk asibitin da muka je sai ace mana wannan bana asibiti bane, na gargajiya ma idan muka je sai ace mana muje asibiti har muka gaji da yawuce-yawuce, daga nan dai aka yiwa baban mu kwatancen gidan wani malami yana can a unguwar nasarawa muka je, baban mu yayi masa bayanin dukkanin abunda ya wakana malamin ya jin-jina kai ya kalle ni sannan yace “kana d'auke-d'auke ne?.


   “A'a bana d'auke-d'auke"

malamin yayi shiru yana nazarin wani abu finally yace “kayi tunani dai, baka ta6a d'aukan kayan wani ba?" Same answer na basa, ya sauk'e sassanyar ajiyar zuciya yace “ba shakka wannan kumburin naka yana da nasaba da wani, amma babu wani abu daya shiga tsakanin ka da wani?" “Allah gafarta malam a gaskiya kusan kullum sai munyi rigima da jama'ar unguwar mu kafin lalurar nan ta same ni".


   “Toh ya zama dole kaje ka bisu d'aya bayan d'aya ka nemi tuba idan Allah yasa wanda yayi ma wannan d'anyen aikin yaji tausayin ka zai war-ware insha Allahu, bayan kwana biyu in kuka babu wani canji sai ku dawo" godiya sosai muka yi masa sannan muka fice. Haka kuwa aka yi duk sai dana bisu d'aya bayan d'aya na nemi gafarar su, alhamdulillahi duk wanda na tunkare shi da maganar yafiya cewa yake ya yafe min duniya da lakhira.


  Bayan kwana biyu babu alamar canji sai muka koma gidan malamin. shiru yayi yana nazari, sosai ya 6ata lokaci a haka daga bisani yayi ajiyar zuciya yace “lallai al-amarin nan babba ne".


   “amma kayi tunani da kyau dai" nayi shiru ni gaba d'aya nama manta da wancan almajirin, ina tunowa da shi naji gabana ya fad'i ras! Take hawaye ya gan-garo min baki na yana rawa nace “ba shakka akwai bare-baren almajirin dana mara kwanakin baya har sai da ya suma, kuma y'an uwan sa sunyi ikirarin cewa sai sun d'auki fansa".


   “Ba-barbare? Tab! Babbar magana" malamin ya fad'a a d'an razane hakan yasa jiki na yayi sanyi matuka “a gaskiya bani da kokwanto suna da alaka da wannan ciwo naka, kuma in kana son lafiya ya zama dole kaje ka nemi yafiyar su dan wallahi kanuran nan suna iya yiwa mutum abunda yafi naka ma, amma kayi tattaki izuwa makarantan nasu ka nemi gafarar su shine kawai mafita a gare ka" godiya sosai mu kayi masa mahaifi na yayi masa d'an dunkuli sannan muka tafi.


    Kamar yadda malamin nan ya shawarce ni da naje can makarantar nasu neman tuba, haka kuwa nayi amma da naje tsangayar da mamaki na, naga babu kowa a makarantar alamun sun tashi kenan, zubewa nayi kasa on my knees ina kukan fitan rai dan kuwa yanzu na dad'a tabbatarwa da kaina cewa ciwo na yana da alaka da wad'annan mutanen ne. A garin ba inda bamu neme su ba amma sam koda d'uriyar su bamu ji ba.


     Gaba d'aya tausayin sa ya shige mu sai tsiyayar da kwalla kawai muke dan wallahi ban ta6a ji ko ganin haka ya faru da wani ba koda kuwa a film ne ballantana a history. “Allah yasa kaffara ne ya kuma yaye ma wannan bala'i shine kawai addu'ar, yanzu dai maghariba ya karato kuma ya kamata mu kyale ka hakan nan kaima ka huta" aliyu yayi maganar yayin da yasa hanky yana wiping off na hawayen sa. 


   “Ameen thummah ameen, nagode! Nagode!! Kwarai da gaske da irin kulawar da kuke nunawa a gare ni, Allah ya saka da alkhairi ya kuma bar zumunci" da “ameen" muka amsa masa sannan muka fice bayan munyi sallama da mahaifiyar sa da sauran mutan gidan. *(Allahu akbar! Ashe dai sallamar mu ta karshe kenan Allah sarki rayuwa, Allah kasa mu cika da imani ameen)*.


     The following day muna da exam na mathsmatics from 9:30㏂ sai 3:00㏘ muka fito daga hall so exhausted ga kuma wani irin fad'uwan gaban da nake ji tun shigan mu cikin hall d'in har muka fito bai daina ba kuma ban san dalili ba, a haka dai muka tsaya da sauran friends namu muka d'an has-haska pictures, a hanya ma muka idar da sallah'n la'asar sannan muka wuce gida. Muna zaune akan d'an benching dake kofar gidan mu nida amini na aliyu sai muka hango keke napep ya shigo layin zuciya ta, ta buga da karfi mai mashin d'in yana wucewa a gaban mu na saki salati saboda mahaifiyar muh'd na hango tana rik'e da tea flask a hannun ta da tabarma.


    Not long enough muka jiyo karan jiniyar amblance yana shigowa ashe tun tafiyar mu makaranta aka d'ebi muh'd sakamakon jikin nasa ya tsananta fiye da kima. Salati kawai muka rinka yi har aka wuce da gawar sa.


    Muka d'ugunzuma izuwa makabarta tare da y'an unguwa, wallahi bakwa bina bashin rantsuwa in dai iri na za'a binne a cikin kabarin wallahi sai dai mutum biyu. Bayan an kawo mamacin ramin yayi masa kad'an ta saman kafad'ar sa sai da aka yi ciko da duwatsu sannan aka jera itatuwa followed by gany'e da kwa6a66iyar kasa da busasshiya sai bayan sallah'r i'sha muka baro makabartan. Allah yasa aljannah ce makomar ka muhammad ameen thummah ameen.

 

Allah yasa mu anfana da wad'annan darussa ameen. Allah muna rok'on ka da kasa mu fi karfin zuk'atan mu, mu kuma cika da kalimatil *la'ilaha il-lal-laa muhammadun rasulullahi sallallahu alaihi wasalam* ameen



```dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah shi kad'an sa malikil quddus, wanda ya ciyar damu, ya shayar damu, ya tufatar damu, ya isar mana. Na rubuta wannan littafi ne dan isar da sako kuma alhamdulillahi na isar, Allah yasa masu irin halayyar sa su gyara dama wad'anda suke yunk'urin bin wannan hanyar ameen. Ya Allah ina neman afuwar ka gare ni bisa kuskure ko tun-tu6en harshe da nayi a bisa rashin sani a dukkanin lamura na, ka bani ladan abunda na fad'a dai-dai ka kuma karamin kaifin basira na rubuta abunda d'umbin jama'a zasu anfana da shi ameen```



 мυsα м sαεεd

  (mr. melody)



   *```WABIHAMDULLAH```*



Complied by Princess Aysha Muhammad (Humaira) 


adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *