Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Saturday, January 30, 2021

Tsuntsu Me Wayo Hausa Novel Complete

adsense here

Tsuntsu Me Wayo Hausa Novel Complete

 [10:00PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

  ( ta wuya ake kamashi)

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*



Biamillahir Rahamanir Rahim




1-3


✏Wata kyakyawar bafulatana ce tafe sai faman sauri take, sakamako wani gaggarimin hadari daya hadu yayi bakin kirin lallai idan ruwannan ya sameta ahanyar nan zata yabawa aya zaki ,gashi ba gida gaba ba gida baya waigawa tayi sosai ta kalli bayanta wani laffiyayyan iska ta hango ya nufuta dan haka ta kwasa da gudu ,amman ina tuni kasa ya cika mata ido  dole ta tsaya tana share idon tana kuka wani kara ta faraji abayanta wanda bata tabaji ba, dan haka ta fara tunanin ko iska takaita wani duniyar daban ne, kara dunkulewa tayi waje daya tana kuka meban tausayi


muryan wasu maza ta faraji akanta daya daga ciki yana fadi ke baki da hankali kinajin mota bazaki kwauce ba.


" shiru tayi batace komai ba "


ya cigaba da magana ke bazaki tashi ba saina sa mota na latse ki dayan ko ban da yan wake waken shi babu abin da yake. jitayi ya sake cewa big boy yariyar nan fah inajin kurma ce.


  da katawa yayi daga wakar da yake rairawa yace 


  " Ok yayi kyau d'aga mun ita mugani ko tana da kayan marmari "


 dariya dayan yayi sannan yace 


  " kai fah matsalar ka kenan ba dama kaga mace sai ranka ya biya"


kama ta yayi ya d'aga ta, tanajin an d'aga ta tafara kokarin guduwa amman rokon da yayi mata bana wasa bane dan haka ta kasa gudu gashi idon ta har yanzon ta kasa budewa bare tasan wacce duniyar iska ta kawo ta, ji tayi yana fadin big boy zo ka duba ta yamma nayi.


 wanda aka kira da suna big boy ne ya fara takowa yana zuwa gaban yariyar yayi birki yana kare mata kallo yana wani ya mutsa baki  zuwa cen yace


  " babu laifi sai dai tayi kankanta da yawa  amman babu komai samun ita amota na d'an matsa ta "


  fashewa tayi da kuka tana tunanin wannan wani gari ne iska ta kawota wanda ake matsa mutane


tanaji suka sakata acikin abun da suka kira da suna mota dan haka kukanta ya karu ,


hannun taji yana yawo asaman kirjinta bige hannun ta fara amman ina karfin namiji da mace ba  daya bane tuni ya yaga rigar dake jikinta ya rage daga ita sai zani uhu take iya karfinta amman kaman dad'a ziga shi take zuwacen ta farajin abu na yawo atsakanin cin yoyinta tun daganan bata kara sanin inda take ba, zuwacen ta farajin hayaniyar mutane akanta wasu daga ciki suna fadin daniju ce yar gidan malam  habu.


itako tana kwance tanajjin su ,wasu suna fadi adauketa akaita gida wasu kuwa cewa sukayi kar ataba ta.


 daker aka samu wata tsuhowa da tace ita zata kaita gida domin kuwa dana kowa ne hijjabin ta ta cire tasawa daniju domin kayan dake jikin ta sun yage ahankali ta riketa sukka nufi cikin gari.


abunka da karamin gari tuni lbr ya isa kauya kafin su isa yara da manya suncika kofar gidan malam habu.


  hayaniyar mutane ne ya fito da malam habu dan dawowar shi daga kasuwa kenan.


sallaman da tsuhuwar tayi shi ya da katar da malam habu cikin mamaki ya kalli daniju dake rike hannun tsuhowa tana dingishi cikin tashin hankali yace


  " ke kuma daga ina Allah yasa ba wani bala,in kika kwaso ba"


daga bayanshi aka bashi amsa ahaiye nanaye yau dai ga abinda muke fada ana karyata mu ai tuni na fada yariyar nan bin maza take amman uwarta ta karyata ni toh yau dai ga zahiri.


  cikin fada malam habu ya daka mata tsawa  tare da fadin badake nake magana ba.


  bayan tsohuwar ta zaunar da daniju sannan ta kalli matar dake kusa da malam tace


   ina mahaifiyar yariyar nan take?


  malam ne ya fara kiran salamatu.


  cikin sauri ta fito idonta cike da hawaye.


 tana daga tsaye ta kasa cewa komai .


tsohuwa ta shiga yi musu bayanin ayanayin da ta same ta.


cikin kuka salamatu tayiwa tsohuwar godiya har kofar gida ta rakota .


  bayan ta koma cikin gidan ne ta isa gaban daniju ta kama ta tanufi bandaki da ita basukai  ga shiga ban dakin ba malam habu yace


  " dakata salamatu "


cikin sauri ta tsaya tajuyo takalleshi.


cikin tashin hakali yace salamatu lokaci yayi da zaki tura yariyar nan wajjen ubanta indai tana dashi, inkuwa ba haka ba zata barmin gida yau dinnan dan bazan yadda ta lalata min tar biyan yara ba.


cikin kuka salamatu ta tsuguna tana ba malam hakuri amman yace ina sam bazai amince ba mikewa yayi ya fara hankad'a daniju kofar gida .


biyosu salamatu tayi tana kuka tana rokan sa yayi hakuri tuni yaran dakke kofar gida suka zagayeta suna mata wakka.


cikin matsanan cin tashin hankali salamatu ta koma cikin gida cikin sauri ta fara hada kayanta dana danijju domin kuwa bazata taba bari daniju ta bar garinnan ita kadaiba gara ta kaita gidan uban ta inyaso saita dawo.


fitowa tayi cikin sauri ta nufi kofar gida malam ya bita da kallo yace


  me kk shirin yi ne?


cikin kuka tace zan kaita katsina ne  gurin babanta.


 atakaice malam yace ban yadda ba babu inda zaki idan ko kika sa kafa kk bar gidannan abakin auren ki.


 murmushin takaici tayi sannan tace babu komai malam na amince domin kuwa fatima itace 'yata kwaya 1 wanda na haifa aduniya dan haka bazan bari ta salwanta ba dan idan na barta batasan inda zata nufaba Allah yasa haka shine mafi alheri.


bece komai ba har tabar gidan ila tashin dariyar baraka da takeji.


    

🕊🕊

_Ummu Yazeed_

                  🕊🕊

[10:00PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

  ( ta wuya ake kamashi)

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*



Biamillahir Rahamanir Rahim




4-5


✏Karfe 4:00pm suka isa gidan su salamatu dake cikin garin katsina, tana, rike da hannunn yarta Fatima,


 salama tayi acikin rauna nanniyar murya.

  wata dattijuwar mata ce ta amsa tare da fadin muryar wa nakeji kamar ta salame.


cikin sauri salamatu ta saki daniju ta rungume matar tana fadi nice dada.


  itama matan kara matseta tayi cikin kuka tace


  " yau Allah ya karbi addu,ar da na dade inayi shekara da shekaru, ta sake cewa me yasa kika tafi kika barmu haba salamatu baki kyauta min ba kin azaftar dani kinsamu cikin ma muyuyacin hali nida mahaifin Fatima, yasha wahala wajen neman ku.


kukan salamatu karuwa yayi, zamewa tayi ta duka kasa tace


  " dada dan Allah ki yafemin ba ason 

raina na aikata haka ba nayi ne dan na gujewa furucin yusuf dan idan na bashi fatima alokacin zan shiga wani hali kuma bansan ya rayuwar ta zata kasan ce a wajen dangin yusuf ba da suka dauki tsana suka daura min, sai kuma gashi wuyar  da na gudar mata beyi tasiri ba dan ayanzu anlalata mata rayuwa cikin kuka ta zaiyanewa dada abinda ya faru.


lallashin ta dada ta shiga yi sannan ta mike ta dafa daniju dake zaune sai tsiyayar da hawaye take tace


  " karki damu fatima insha Allahu Allah saiya saka miki kuma yabi miki hakkin ki da izinin allah"


itadai fatima batace komai ba illah share hawaye da take.


mikewa dada tayi ta hada ruwan zafi ta kai ban daki sannan ta dawo ta daga fatima da kanta tayiwa fatima wanka .


bayan sun fito dada ta kwance daurin kayan da suka taho dashi ta zabi me dan dama dama ta mikawa Fatima


  sannan ta nemi guri ta zauna ta shiga tunanin lallai idan yusuf ya samu lbrn dawowar salame ba karamin farin ciki zaiyi ba domin kuwa ya dauki son duniya ya daura akan fatima.



    *Tushen Labarin*


Alhj salisu asalin dan jahar katsina ne kuma shahararren dan kasuwa, zaiyi wuya alissafa yan kasuwa 5 ba asa sunan shi ba.


  yana da mata 1 da yaranshi maza 2, kasancewan Allah be bashi haihuwa da yawa ba ya taso yana matukar kyaunan yaranshi 2 da Allah ya bashi kasim shine babba wanda ayanzon haka yana da aure yaranshi 3, sai yusuf wanda ya kasance mahaifin fatima.


itako salamatu mahaifiyar fatima, mahaifin ta ya kasance me gadi agidan alhj salisu dan haka lokacin da yasuf ya furta wa mahaifin shi yana son auren salame yaki amincewa.


acewarshi bazai taba bari dan shi ya auri yar me gadin gidan shi ba.


mahaiyar salamatu ta kasance bafulatana ce dan haka salamatu ta kwaso kamannin mahaifiyar ta.


shikuwa yusuf wani irin soyayya yake wa salame Wanda har takaiga kinjin maganar mahaifin shi 


 " lokacin da alhj salisu ya lura dan nashi yana da niyar nijire mishi sai ya yanke hukuncin koran baba megadi.


  haka ko akayi malam bello ya shiga tashin hankali lokacin da me gidan nashi ya gayamai ya sallame shi.


  kudi ya bashi masu yawa dan haka ya nemi wani dankaramin gida ya saya .


  duk da haka yusuf be hakura ba saida ya bisu har gidan da suka koma 


wasu mutane ya samu ya kaisu amatsayin yan uwan mahaifin shi suka nemar mai auren salamatu.


  bayan an daura musu aure ta tare batare da sanin dagin shi ba.


bayan shekara daya ta haifiyar ta mace wadda yasa mata sunan mahaifiyar shi wato fatima fatima nada wata uku alhj salisu ya samu lbr dan haka ya dira gidan   , yusuf yaji mamakin yadda akayi ya gano gidan 


yayi mishi umarni da ya saki salame ko kuma ya sallama shi, cikin rawan baki yusuf ya saki salamatu yana kuka tana kuka suka rabu da goyon fatima abayan ta, gidan iyayenta ta nufa bayan wasu kwanaki alhj salisu da kansa yaje har gidan su ya jaddada musu dazaran Fatima ta isa yaye zasu karbeta dan haka salame ta daukki yar ta ta bar garin.


 guduwa salamatu da ya tada hankalin family alhj salisu domin kuwa suna matukkar bukatan yara , shikowa yusuf yafi kowa gargiza dan haka har yanzo be kara maganar aure ba iyayen nashi ko sunyi mgn sungaji.


bayan salamatu ta isa kano acinkin wani akauye ana kiran sa mai giginya bata kara marmari komawa gida ba agidan me unguwa aka sauketa bayan wani lokaci ta samu mijin aure wato malam habu.


  lokacin da ta aure malam habu tasame shi yana da uwar gidan shi me suna baraka tasha matukar wahala awajen baraka ita da yarta fatima zagi iri iri babu wanda ba,ayi musu ba ita ta Fara kira fatima da suna daniju saboda tsabar bakin cikin cikin da takeyi da ita kuma sai sunnan ya beta acikin kyauyen.


   kazafi kuwa kullum cikinyin sa take


*Cigaban Labarin*


 bayan fatima ta gama shiryawa direct gadon dada ta nufa ta kwanta tana mai bakin cikin abun da ya faru da ita.


   sai dare malam ya shigo gida ya tararda abinda ya cire tsanmani woto salamatu da jikar shi fatima .


  bayan kwana 2 dada ta kira salamatu bayan ta zauna tace


   " nakiraki ne domin na fada miki shawaran da muka yanke da baban ki kuma dole ne ki daure ko ya miki dadi ko be miki ba"

   baffan ki yace yau dinnan akai fatima gidan kakan ta, saboda idan suka samu lbrn dawowar ki batare da munfada musu ba zasu zargemu kuma dama kyawun da gidan uban sa.

  

  ahankali ta bude baki tace shi kenan Allah yasa haka shine maffi alheri.

 

  fitowa tayi ta leka dakin da fatima take taga sai hada kaya take, ahankali ta kira sunan ta ta dago ta kalleta tace


   " karki dauke komai daya danganci kayan sakawa naga sai wani rawar jiki kikeyi"


   turo baki fatima tayi sannan tace toh mama ba dole nayi rawar jiki ba, ban fah taba ganin babana ba  kuma idan na tafi babu kaya wani kayan zan rinka sakawa.


murmushi mama tayi sannan tace fatima kenan ai wannan kayan naki ko goge kitchen din su bazasuyi dashi ba dan gida ne namasu hali, babanki kuwa harsai kingaji da ganin sa , dan nasan idan ya ganki bazai kuma bari kizo gurina ba, dan haka zanci gaba da miki andu,a Allah tsareki aduk inda kk



   maganar dada sukaji dana fadin toh fatima fito mu tafi.


  cikin sauri ta fito domin kuwa bakaramin kosawa tayi ba tana tafiya tana fadin mama na tafi 


   toh kawai salamatu ta iya furtawa  zuwacen ta kira sunan fatima ta dawo ta tsaya tace gani


  ahankali tace kicewa babanki inagaida shi

 

toh kwai tace tabi bayan dada aguje,


suna fita ta saki kuka me ban tausayi.




🕊🕊

Ummu Yazeed

               🕊🕊

[10:00PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

  ( ta wuya ake kamashi)

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

:        *_Fadeela Lamido_*




9-11

Tafe suke kowa yayi shiru babu mema wani magana salis ne ke jan motar yayin da taslim  take gefenshi daddy da ummi ko suna baya sunyi shiru kowa da kalan tunanin shi duk da dai baya wuce tunanin dansu suke wato haydar dan uwan haihuwan salis, da haka suka isa gidan, salis nayin pakin taslim ta fita da gudu tayi cikin gidan.


  bin bayan ta sukayi     suna shiga suka sameta ta kwakume fatima tana kelketa dariya yayin da fatima kebinta da kallo tana murmushi.


 yadidko ce ta fito daga daki tana fadin muryar wa nakeji, daidai lokacin iyayen suka shigo ummi ce ta kalli fatima tace


  taho nan yata bayan ta zauna tazo gabanta ta zauna Hannun ta tasa ta kwatar da ita jikinta tana shafa kanta yadidko nakallon su tana murmushi.


  taslim tace ummi muwuce da ita gida.


  kafin ummi tayi magana yadidko tace ina aibaku isaba nan zata zauna.


  " sai alokacin salis yayi magana danshi baifaye surutuba ahankali yace


   " kunjita saikace ke kika haifet.....

 

bekai ga karasawaba daddy ya dakatar dashi da fadin kafara ko ?


  yadidko tace barshi yayi ai bashi da kunya waima ina daya fitsararren ne?


 shiru daddy yayi yasa kan sa akasa sai ummi ce tace yana cen wajen gantalin sa.


  fada yadidko ta farawa ummi tace


   " karna sake jin kince masa gantalalle kefa uwace addu,a ne ya dace dake ba mugayen kalamai ba Haba aiko dan sunan mahaifinki da yake dashi kyaraga masa.


   kan ummi akasa tace toh nabari hjy.


  suna cikin haka alhj yusuf ya shigo da kaya riki riki acikin manyan ledoji.


  salis ne ya mike ya karfi kayan 


alhj yasuf yace

 kasa kayan amotar ku kayan kanwar ka ne gobe sai kakai mata dinki.


 cikin sauri taslim tace baba yaufa da sister fatima zamu tafi.


   murmushi yayi sannan yace Allah ya bada sa,a taslim.


mikewa tayi ta daka tsalle sannan tayiwa yadidko l gwalo .


  murmushi dada tayi sannan tace ja,ira zanyi maganinki ne.


mikewa daddy yayi yayiwa mahaifiyar shi sallama sannan ya kalli ummi yace idan kungama ku fito 

yana fadin haka ya juya ya fita. alhj yusuf ne ya mike yabi bayanshi.


  bayan kamar 11 minutes suma suka fito harda fatima.


   bayan sun isa gida taslim da fatima daki daya suka kwana.


  the next day

     9:5am

daddy ne ya tura  kofar dakin su salis ahankali ya shiga ganin shi yayi zaune yana karatun alkur,ani zuwa yayi dafdashi ya zauna.


  salis ya juyo yakalleshi ya rufe kur,anin sannan yace inkwana daddy?


  cikin fara,a daddy yace lfy lau babana, saidai abu daya dake damu danyau nakwana banyi bacciba idai kunne na yajimin gaskiya toh lallai haydar bekwana gida ba dan banji shigowar shi ba .


    shiru salis yayi yasa kansa akasa.


  daddy yasake cewa babana gayamin komai karka boyemin dama haydar ya saba kwana awajje ne?


  kai ya daga alamar eh.


  shiru daddy yayi nadan wani lokaci zuwacen ya dago yace mamanku ta sani ?


  nanma daga kkai yayi


  daddy yace toh yayi kyau, kunyi waya dashi ne.


 kasan akasa yace a,a


  toh kanemeshi awaya idan kasame shi kacemai nace idan ya wuce 2 hours be dawo gida ba ya neme wani uban.


cikin sauri ya juya ya fita adakin.


  mikewa salis yayi ya dauki wayar shi ya fara neman layin haydar zuwace aka dauki wayar saidai abinda ya bashi mamaki muryar mace yaji cikin lankwasa harshe tace waye



  shiru yayi nadan wani lokaci sannan yace iname wayar yake.


  itama kamar bazatai mgn ba tace yana bacci, 


cikin takaice ya kashi wayar yamike ya fara shiri zuwa Office.


  yana kokarin fita agidan yaci karo da alhaji yana shigowa yace kasameshi kuwa?


  cikin sauri yace a,a daddy bansame shi ba amman zuwa anjima zankara gwaawa.


4:02pm salis ya dawo gida yana ardu,a azuciyar shi Allah yasa haydar ya dawo.


  afalo ya samu taslim da fatima suma kallon wani film a TV, fatima ya gani tasa wasu kaya masu kyau riga da siket na atamfa bakaramin kyau suka mata ba ya dade tsaye yana kare mata kallo suko hankalin su na wajen kallo hannun shi yasa acikin aljihun shi sannan yayi magana ahankali yace sister zahra.


dukkan su suka juyo suka kalleshi murmushi fatima tayi taslim tace yaya yaushe kashigo?


  zuwa yayi dafda fatima ya zauna sannan yace zahara kinga yadda kikayi kyau kuwa.


  cikin sauri taslim tace nifa yaya?


kema kinyi kyau amman zahara ta fiki kyau, tsaki yaja sannan yace haydar ya dawo kuwa.


  nidai bansani ba ammafa kamar be dawowa ba.


  mikewa yayi sannan yace kuje Ku shirya na kaiku kuyi gidan alhj


  da gudu taslim ta tashi ta shige daki fatima ma mikewa tayi tabi bayan ta sumi sumi dan har yanzon bata gama sabawa da gidan ba.


bayan sungama shiryawa taslim tace nidai fatima ki sameni dakin yaya.


  bayan fatima ta saka hijjabinta tace ummi mun tafi murmushi tayi sannan tace adawo lfy fatima.


  tana fitowa falo ta hango salis kwance akan kujera idonshi rufe saidai abida ya bata mamaki kananan kayane jikinshi sun matseshi kuma daidai da takalminshi be cireba dashi ya kwanta kara matsowa tayi ta kalli shi sosai wani gashhi ne cike akan sa cibiri cibiri irin na samarin zamani tabe baki tayi sannan tace azuceyar ta toh ina taslim tayi, 

gani tayi bata da mafita dole ta tasheshi wata kela ita suke jira gashi yaci uban kwalliya dan hakka ta matsa dafdashi tace yaya katashi muje nagama fah.


  ahaukaci ya bude ido yakai mata tokari aciki ,cikin sauri ta duka ta rike cikin



matsowa ya Farayi yana fadin dan kutumar uban ki wacece ke dazaki zo ki tadani ina bacci.


  a sittin ta mike rike da ciki tayi dakin




    🕊🕊

Mmn Yazeed

            🕊🕊

[10:00PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

  ( ta wuya ake kamashi)

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*




12 -14



Ummi na kwace akan gado taga fatima rike da ciki arude ta diro da kafafuwan ta tace


   " fatima lfy me ya sameki aciki ?


  kasa magana tayi illa kuka da ta keyi.


 ummi ce ta kamota ta kwantar da ita jikinta tana rarrashinta ,ta gayamata me yasame ta 


daidai lokacin salis da taslim suka shigo dakin, salis yace sister ya haka muna ta  jiran ki kuma kinki fitowa,


 kallonta yayi sosai yaga ashema kuka take ya sake cewa ummi me ya sameta.


nima abinda nake tambayanta kenan taki magana.


  tsugunawa yayi gaban su yace sister gayamin me ya sameki?


  cikin mamaki take kallon salis azuciyar ta tace lallai wannan munafiki ne wato har yaje ya cenzo kaya dan tsabar mugun ta ahankali ta dago jajayen idonta ta harare shi sannan tace 


   bakai bane kasa kafar ka ka naushe ni aciki.


    zaro ido yayi sannan yace ni kuma ? gaskiya bani bane ,sister toh me kikamin da zan dake ki?


  ummi ta kalli salis tace haydar ya dawo ne?


  Ok eh ummi sanda muka fita nida taslim naga shigowan shi.


batace komai ba ta mike ta fita adakin salis ya matsa gabanta ya kamo hannun ta yana wasa da yatsuta yace kiyi hakuri, zahara bani bane kisan mu yan biyu ne kuma muna matukar kama  nan gaba kad'an zaki fara banbance mu dan akwai dan banbanci, 

kallon idonta yayi sannan yayi murmushi yace ban da abinki ma sister ai shigar mu ba iri daya bace shi bakiga ya tara gashi bane saikace mahaukaci.


 taslim ce ta saki dariya tace wlh brother ni yanzon ma tsoro yake bani haka ranar nan daga naje wucewa ta kusa dashi lokacin yana waya saiji nayi ya jifeni da cup wai nazo naji abinda yake cewa ne naje na gayawa ummi.


 salis yace ai yana da matsala haka dai zakuita hakuri dashi.


  ji sukayi anturo kofar ummi na gaba haydar na bin ta abaya zuwa yayi ya tsuguna agaban fatima kamar yadda yaga salis yayi kamar me ciwon baki yayi mgn ahankali sister kiyi hakuri na manta acemin kina gidan nan na dauka wata ce daban.


   shiru tayi ko kallon shi batayi ba sai dai ko ahaka ta gane banbancin murya atsakkanin su domin kuwa muryar salis tafi na haydar sanyi.


  jinda yayi tayi shiru yasa ya waiga ya kalli salis yace brother katayani bata hakuri 


  salis yace bakumai haydar ya wuce sai dai akiyaye gaba.


  sai alokacin haydar ya kalli fatima daniyar yayi mata godiya amman yana kallon fuskarta ya kasa cewa komai sakamokon muguwar kama da tayi masa da wata yariya da yake marmarin sake kasan cewa da ita


mikewa yayi cikin sauri ya nufi kofa dukkansu binshi sukayi da kallo ummi ce tace ikon allah, Allah ka shirya wannan bawa naka


 salia ko mikewa yayi daga gaban fatima yana fadin toh yanzo dai shikenan haydar ya hanamu fita.


  

  Haydar na fita ya nufi dakin mahaifin shi kamar yadda ummi ta umarceshi ahankali ya tura kofar ya shiga neman guri yayi ya zauna sannan ya daga kai ya dubi mahaifin shi dake zaune yana karatun jarida, ahankali yace



    " daddy ina yuni?


  baza yayi dashi kamar ma besan da shigowar shiba zuwa cen yace a inakakwana?


 kanshi akasa yace daddy mun je zaria ne muna kan hanyar mu ta dawowa motar ta lalace amman dan Allah kayi hakuri bazan....


tsawa ya daka mishi wanda yasa dole yayi shiru sannan yace Karka maidani mutumin banza haydar guda nawa kake, nine ubanka babu wani dubara da zakamin, batun yauba na kula kai mutumin banza ne, toh bari kaji daga yau kar magriba ta sake maka awaje kuma daga office ban amince ka wuce ko Ina ba kanajina ?


  eh kawai ya iya furtawa domin hukuncin yayi masa tsauri.


  da daddare salis ne zaune adakin su yana karatun Qur,ani yayin  da haydar ke kwance akan gado sai juyi ya keyi.


 zuwacen salis ya rufe Qur,anin ya iso bakin gadon ya zauna sannan yace


  " brother meke damun ka ne naga sai juyi kake?


  tashi yayi ya zauna sannan yace kasan matsalata brother bana iya bacci ni d'aya.


murmushin takaice salis yayi sannan yace haydar al,amarin ka yana bani mamaki kai wai bakajin tsoron Allah ne, ga hanya mafi sauki kabi kaki sai anyi amma mgn kacei Allah ne ya daura maka toh naji Allah ne ya daura maka kayi aure mana, ko mata hudu ne kana iya hadawa.


hannu haydar ya dagawa salis haba wai kai sai ka rinka cewa nayi aure duka duka guda nawa nake ko 30 years ban hadaba fah.


  kulewa salis yayi cikin fada yace kananufin sai mutun yakai 30 sannan zaiyi aure wani malamin ne ya fada maka?


  nidai kawai ka rufamin asiri na dan fita da suba zandawo.


cikin fada salis yace wlh bazan rufama ba kana fita zan fadawa daddy


tsaki haydar yaja ya tura kanshi cikin bargo yana fadin muna fuki kawai


 naji ni munafuki ne kaikuma dan iska me lalata yaran muta ne.


  hankade bargon yaye ya duro ya cefkke wuyar rigar salis nan danan dabe ya kyaure atsakanin su.


  ummi da yan matanta suna falo suna kallon wani film suka farajiyu hayaniyar su aguje suka nufi dakin.


  salis naganin su ya tsaya cek amman haydar be daina kaimai doka ba.


  ummi ce ta fara kokarin jan haydar tana cewa haydar duk yadda akayi kana shan kayan maye ka rasa dawa zakayi fada saida dan uwanka innalillahi wa ina ilaihir raju, un.


  salis ne yazo ya rike ummi yana fadin ummi jeki abinki ya wuce taslim zahra kuje ku kwanta.


  ummi kuka takeyi dan haka su fatima suka fara kuka.


  shiko haydar sai maida numfashi yake yana hararar salis ya koma bakin gado ya zauna.


  salis ko ganin ummi tana kuka hankalin shi ya tashi, yayi daya sanin biyewa haydar yace ummi dan Allah kije ki kwanta babu abinda zai sake faruwa.

suna fita haydar ya mike ya koma kujera ya zauna hannu yasa a aljihunshi ya dauko sigari ya kunna ya fara zuka yana fesar da da hayakin




🕊🕊

Mmn Yazeed

           🕊🕊


  Comment 07014197556

[10:00PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

  ( ta wuya ake kamashi)

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*



15 - 16



 Salis tsaya wa yayi yabishi da kallo cikin mamaki yasan haydar yana shen sigari tunda yasha gani amotar shi amman betaba sha agaban shiba sai yau ,


filo ya dauka ya nufi falo dan baxai iya shakan wannnan warin ba.


  washegari


salis yakai fatima makaranta secondary akasata jss 1  

   itako taslim tuni ta kare secondary ayanzo haka tana cigaba da karatu, dan haka kullum salis kekai fatima makaran ta drive kuma ya dakota saboda lokacin salis yana gurin aiki.


  shakuwa ce tashiga tsakanin salis da fatima me karfi dan ayanzon har fatima ta saki jikin ta dashi sosai.



  shiko haydar tun ranar  da su kai hayaniya da salis kwata kwata baya mai maga gashi har an hada one week amman daddy yake cire takunkumin shi saima kara samai ido da yake haka kullum zaita juyin shi akan gado sai dai salis yayi tsaki ya juyamai baya dan haka abin ya fara damun shi.


   yauma kamar kullum haydar ne kwance agado rike da ciki yana murkusu ya hada uban zufa.


  salis ne ya taro kofar ya shigo kallon haydar yayi cikin sauri ya karasa bakin gadon yace make damunka.


  daker ya iya bude baki yace cikina ne.


  mikewa yayi ya nufi kofa ahankali haydar ya kirashi bayan ya dawo yace Ina zaka.


  zan fadawa daddy ne.


  zaro ido haydar yayi yace dan Allah karka gayamai  nasha magani zuwa anjima zai sauka.


  shiru salis yayi ya zauna abakin gadon ganin inda haydar yake hada zufa ya sake mikewa ya kunna mai A.C amman duk da haka zufa yake zuwa cen hawaye ya fara zubowa a idon shi hannun shi kuwa yana kasan cikin shi yana dan matsawa 

zuwa cen bacci ya kwashe shi.


   ajiyan zuciya salis  yayi sannan ya gyara kwanciyar shi .


  washegari


 sunfito cikin shirin su na tafiya Office salis ya kalli haydar yace au me ciwon ciki ya cikin naka?


  tsaki haydar yayi sannan yace sai yanzon zaka tambaye ni.


  fashewa yayi da dariya sannan yace


   " wlh brother mamaki kake mani jibeka one week kawai dobi inda kayi zuro zuro, kasan Allah kamata yayi ahada maka mata hadu dan  daya ta maka kadan.


 tsaki haydar yayi ya shege motar shi yabar wajen.


 yana isa Office yayi amfani da wayar shi ya kira babban aminin shi anas, 


ba ajima ba anas ya shigo, wata budurwa nabinshi abaya.


 haydar naganin su ya miki yariyar ya rungumo yana kissing dinta itama yariyar yar duniya ce dan tuni ta fara aika mai da makata nan suka lalace.


  jin nurfarfashin da haydar keyi yasa anas barin office din  dan yasan idan ya zauna zasu tasomai da tsumin sa.


 saida ya kwashi awa 3 yana zaune abakin office din sannan yamike ya tura kofar ya shiga ganin yariyar yayi kwance tana barci akan kujeran dake cikin office din tayi matashi da cinyar haidar shima bacci yakeyi hannun shi acikin rigarta..


  hannun shi ya hada yayi tafi nan danan suka mike anas yace toh waikai yau baka da aiki ne, tsaki yaja sannan yace bar aikin nan gobe nayi, juyawa yayi ya kalli yariya yace 


  babyna naga alamar kin

 gaji da yawa yau nabaki wahala am sorry nayi missing dinki ne dawa.


  cikin shagwa tace zani gida nayi wanka na kwanta.


  OK baby badamuwa anas zai maidake gida amdai gobe zaki dawo KO, saboda kar mukuma samun irin matsalar yau.


cikin shagwaba ta mike tana buga kafa kamar zatai kuka take mgn ciki ciki


haydar kara rudewa yayi dan yana balakin son yaga mace na irin wannan shagwabar bare wannan yariyar da komai dake jikinta rawa yake besan lokacin daya isa gareta ba ya zura bakinshi cikin nata saida yayi son ransa sannan yabarta.


karfe 4:00 hayadar ya baro office cike da farin da walwala domin yau ya samu abinda zuciyar shi take muradi yana shiga gida ya samu salis da fatima suta hira suna dariya.



bebi ta kansuba ya shige daki bayan yayi wanka ya biya basussukan sallah da ake binshi ya fito falo .


  suna nan yadda ya barsu saidai ayanzon harda taslim, zama yayi agefe ya kure fatima da ido shi dai yana ganin kamar yasan yariyar nan, idan ma ba itabace toh sunada dankantaka tv ya kurawa ido amman lokaci zuwa lokaci yana satar kallon fatima.


  zuwacen taslim tace fatima kitashi muje gidan yadidko.


 salis yayi karaf yace ke bazata ba ni banason yawace yawace.


 cikin sanyin murya taslin tace haba yaya gidan yadidkon ne yawace yawace kuma fa bajimawa zamuyi ba.


  kalon fatima salis yayi cikin ido yace zahra kinason zuwane?


 cikin sauri fatima ta dukar dakai dumin duk lokacin data kalli cikin idon salis saitaji gabanta ya fadi.


 riko hannunta yayi tabi hannun shi da kallo yana wasa da yatsun yake fadin idan kinason zuwa ki tashi kuje amman karki irin shigar taslim, kisa hijjab ne kuma karku dade.


 da mamaki taslim take kallon salis shima haydar shi yake kallo .


  suna fita haydar yadawo dafda salis ya zauna yace


  " brother kardai son yariyar nan kake?


  a,a haba meka  gani, kodan nace tasa hijjab dama shiyasa naga kana kallo na.


 hannu haydar ya daga mai kaga malam bawani kwana kwana da zakamin ka fito fili kace sonta kake.


 dariya sosai salis yayi sannan yace ni dai bance maka inasonta ba nidai kawai nasan yariyar tana birgeni kuma idan muna tare ina samun kaina cikin nishadi har inji manason mu rabu.


 shine zakace bason ta kake ba wlh sonta kakeyi kuma wlh bazaka aureta ba.


 murmushi yayi sannan yace tunda kaine ubana ba


  mikewa haydar yayi sannan yace

 sai kawai friends din na suga wannan yariyar amatsayin amaryar ka aisai sumin dariya idan bazaka iya fita ka nemo mata ba ka bari ni zannemo maka.


 dariya salis yayi  sannan yace ni kuma narasa wanda zai nemomin mata sai wanda ya kauce hanya


azuciye haydar ya miki daidai lokacin su fatima suka fito cikin shirin tafiya dan haka yadan tsaya.


kallon su yayi ya yamutsa baki saboda ganin su sanyi da hajjab har taslim shiko salis sai mumushi yake yace gaski kunyi kyau takawa yayi zuwa gaban fatima ya daga hannu shi daidai fuskar ta yana kokarin cire mata wani dan zare daga jikin hijjabin bayan ya cire zaran yakai bakin sa daidai kunnen ta yana mata mgn acikin taslim da haydar babu mejin me yake cemata saidai fuskarshi tana dauke da murmushi yayin da fatima ta kamo hijjab dinta ta rufe fuskarta tana dariya.


   haydar ya kara kulewa kuma lallai yanason yasan me salis ya fadawa yariyar nan har take dariya, tana nufin itama tasan love ne yar kauye da ita wani dubara ne ya fado masa cikin sauri ya nufi kofa yana fadin kuzo muje nakaiku



🕊🕊

Mmn Yazeed

             🕊🕊🕊

[10:00PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

        🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*



*Gaisuwa ta musamman ga duk wanda yake cikin wannan group  *Farfazaz novels* _kunfi ko wani group comment da nuna soyayyar ku akan wannan lbr Tsuntsu me wayo inajin dadin kasan cewa daku_ 💃💃💃😘



21 - 23



Zama yayi nesa da salis kanshi akasa dan duk abin shi yana tsoron daddy shi ahankali yace gani.


  daddy ya dago ya kalleshi yasa hannu ya cire gilas din dake idon shi sannan yace me ya had'a ku ?

  

  d'ago kai yayi ya kalli salis ya sake mayar da kanshi kasa yayi shiru.


 ummi tace wai ba dakai ake mgn ba ne


  bece komai ba kuma har yanzo kansa na kasa.


  daddy yace kyale su tun da bazasu fada ba ai sunfi kusa, amman nasan haydar ne baidan gsky wata kila ka kule shi ne amman ni araina banason kuraba daki nafiso sai kunyi aure kowa ya samu abokiyar zama ko ya kuka gani?


   haydar ne ya fara magana daddy ai ko munyi aure gida daya zamu zauna.


  cikin sauri salis yace dawa dakai Allah ya kiyaye wlh ba zan zauna dakai ba.


  sakin baki haydar yayi yana kallon salis sannan yace salis nine fah.


 fuskar salis adaure yace kaidin fah ina hauka ne zan zauna dakai.


  daga daddy har ummi basuji dadin maganar salis ba, 


 ummi ta juyo da kallon ta gurin salis tace 


 " ni bansan ka da fushi haka ba banji dadin mgnr ka ba idan baka zauna da dan uwan kaba dawa zaka zauna banajin dadin ganin ku cikin wannan halin dan Allah ku zauna lfy.


  juyawa tayi gurin haydar ta harareshi sannan tace kai kuma kabashi hakuri dan nasan kaine mara gaskiya.


   ahankali yace kayi hakuri in Allah ya yarda bazan kara ba.


  har yanzon fuskar salis adaure take dan haka daddy ya kira su gaban shi kama hannun su yayi ya hada yace ya wuce kutashi ku tafi.


  suna rike da hannun juna suka fita.


  ummi ta dawo da kallonta gurin daddy sannan tace


   " salis akwai hakuri amman idan ransa ya baci be iya fushi ba shiko haydar idan be nemi fitana ba bayajin dadi.


  ajiyar zuciya daddy yayi sannan yace Allah ya shirye su.


  haka rayuwa taci gaba da kasancewa agidan alhj kasim tsakanin salis da haydar yau ayi fada gobe ashirya zuwa anjjima  kaga kamar basune suka yi ba.


  kwanci tashi ba wuya wajan Allah dan yanzon kusan shekara fatima uku aku agidan, zuwa wannan lokacin shakuwa ce me karfe tsakanin fatima da salis.


 yayin da haydar ya hura wutar kiyayar fatima azuciyar shi dan ko mgn bata hadasu da ita


  duk da cewa ayanzon idan ka kalli fatima baza taba cewa tayi zaman kauye ba 


acin wad'an nan shekarun so daya babanta ya kaita gurin mahaifiyar ta yanzon  fatima tana ajin karshi na secondary sakamakon kwanya da Allah ya bata.


   ta bangaren ummi kuwa wato mahaifiyar su haydar bata nunawa fatima wani banbanci tsakanin ta dasu haydar dan haka tana cikin kwanciyar hankali matsalar ta daya haydar.


ayanzun dai fatima ta zama cikekiyar budurwa komai na jikin ta ya fito sosai 


  fatima ce kwace jikin kakarta yadidko tana danna waya yayin da taslim tana gefe tana cin abinci suna fira da taslim.


  sallaman alhj yusuf ya katsa musu hira, bayan yazaunaya kalli fatima  dake jikin mahaifiyar shi yace ke ashe baki da hankali katuwarki dake zaki kwanta mata ajiki, yajuya ya kalli taslim sannan yace ke kuma bakiyi mata fada.


  murmushi taslim tayi sannan tace baba tausa fah take mata.


  hararanta yayi sannan yace wai ma me kukeyi agidan nan yau kusan 3 days kenan inaganin ku anan ku koma gidan ku mana.


   taslim ce ta amasa munzo tayata zama ne ai yauma zamu wuce.


   yace gara dai kutafi hira sukaci gaba dayi shi da yadidko.


   zuwa cen su fatima suka fito cikin shirin ta fiya alhj yusuf ne ya kawosu har gida bayan sun gaisa da ummi ya wuce.


   washegari fatima nata zuba ido taga shigowar salis har wan 12 na rana bata ganshi ba dan haka ta shiga neman layin shi saida ta kira su uku ba adauka ba dan haka tashiga damuwa.


   lokacin da taslim ta kawo musu abincin rana kasa ci tayi tana juya cukalin.


  taslim tace sister wai meke damun ki tun jiya naga duk kinyi wani iri.


   meko ni bawani abunda yake damu na.


  taslim shiru tayi taci gaba da cin abincin ta.


  bayan sungama dakin ummi suka nufa suna shiga fatima tace


   ummi wai yaya salis baya nanne?


  eh bayanan bakuyi waya bane halan?


  tace nakirashi yaki dagawa.


ummi tayi murmushi tace kila baya kusa da wayar ne, munyi waya danzon yace min suna hanya.


   dariya taslim tayi tace dama shi yasa kika ki cin abinci wai ku soyayya kuke ne?


 fatima ce ta harari taslim sannan tace wani irin soyayya.


  ummi tace ke rabu da ita neman mgn ne da ita.


  dariya taslim ta sakeyi sannan tace wlh ummi soyayya sukeyi.


  daure fuska ummi tayi sannan tace wai taslim ina wasa dake ne nace kibar mgnr ina ruwanki da su.


  hannu tasa ta rufe bakinta sannan tace na bari ummi.


  daidai lokacin salis da haydar suka shigo bayan sun gaisa da ummi fatima gaida su haydar kadai ne ya amsa shima dan yaga ummi ne hakalin fatima ya kara tashi idonta ya cika da hawaye


 ummi ta lura da halin da fatima take ciki  bata dai ce komai ba dan bata faye son shiga tsakanin su ba


basu dade ba suka fita zuwa dakin su, fatima ko na gefe tayi tagumi.


   ummi ta juya ta kalleta tace


  fatima cire tagumin nan tashi maza ki kai musu abinci.


  har ta dauki abincin ta tuna salis beson ya ganta babu hijjab dan haka ta koma dakin ummi ta dauki hijjab ta fita.


 samun su tayi zaune haydar na nunawa salis wani abu acikin wayar shi sunata dariya aje abincin tayi tajuya har takai kofa haydar yace ke dauki ledar cen ki kaiwa ummi.


    dawowa tayi ta dauka ta fita, kafin takai dakin ummi hayawaye ya fara zubo mata saida ta share hawayen ta shiga dakin ummi ta aje ledar ta koma kusa da taslim ta zauna ummi ta bita da kallo batace komai ba ta mike ta fita.


 dakin su haydar ta shiga cikin mamaki

 suke kallonta.

    kallon salis tayi sannan tace waikai yaushe aka daura maka aure da fatima ne bansani ba


 da mamaki yace ummi bangane me kk nufiba.


 aidama bazaka gane ba kawai dan fatima ta tafi gidan hajiya bata fada makaba kk wannan fushin, matarka ce?


   da sauri ya girgiza Kai.

ummi ta sake cewa toh karage wadan nan dokokin takasa mata suyi yawa kuma kazo ka rarasheta


adakin su ya sameta tana kwance tayi rufda ciki ahankali ya kira sunan ta amsawa tayi batare data waigo ba ya sake cewa toh tashin mana.


   kintashi tayi dan batason yaga idon ta

  gaban gadon yaje ya zauna yace zahara tashi mana kosai nakira ummi ne?


tanajin ya kira sunan ummi ta miki ta fara sakkowa daga gadon binta yayi da kallo dan rabon da ya ganta babu hijjabi ya manta sai yaga ta kara kyau bayan ta zauna ya kalleta yace wato abin harda su kuka?


 cikin muryan kuka tace toh bakai bane kake fushi dani.


   cikin sauri yace nabari indai nine banason nasake ganin hawayen ki 


daidai lokacin haydar ya shigo dakin abakin kofa ya tsa dan haka salis ne kawai yaga shigowan shi


juyawa yayi barayin fatima yace tashi muje gurin ummi.


  tana mikewa yace toh kisa hijjab mana.


  buga kafa ta fara kamar karamar yarinya cikkin shagwaba tace ni gaskiya a,a nan da dakin ummi saina saka hiijjbi.


binta yayi da kallo zuwacen yayi murmushi yace ji abinda kikeyi saikace wata karamar yarinya 


  kara shagwabewa tayi 


   haydar ko dake bakin kofa tuni ya Fara rikicewa dan babu abinda yafi tayar mai da hankali kamar yaga mace tana wannan shagwaban, idon shi nakan kirjinta 


    salis kuwa ji yake kamar ya rungumita dan betabajin irin yanayin da yaji yau ba, juyawa yayi ya kalli haydar yace waikai wani gulman ne ya kawoka


    sai alokacin fatima tasan da shigowan haydar juyar da kallonta tayi gareshi 


  yace ke dena kallona munafuka kawai me suffar aljanu


  salis yakalleshi ya karasa gaban shi sannan  yace muje  


    *******

da daddare duk yan gidan ne suka hadu a falon daddy suna hira zuwa cen daddy yace mun kusa shan biki agidan nan.


   Ummita tace dama kuwa inason nama magana tunda su sunki yi .

 cikin sauri salis yamike zaibar wajen. alhj yace inakuma zaka dawo ka zauna 


  bayan yazauna daddy yace yakamata kuyi aure salis kaida nake ma ganin ka kamar me hankali.


  ummi tace alhaji ai haydar zakawa mgn shi yariga ya kama tashi gatanan kusa da kai duk da dai ba fada sukayi ba amman duk me hakali yasan sun amice da juna


   murna ce ta kama daddy yace toh shine ni baki sanar min ba


  dawai inajira ne su fada da bakin su gatanan ansa mata takunkumi zama da hijjab saikace matar liman 


  taslima ta kwashe da dariya shikuwa salis tunda ya dukar da kansa ya kasa dagowa fatima ma tana kudun dune cikin hajjabin ta


  daddy yajuyar da kallon shi ga haydar yace kaifah


  Sosa keya yayi sannan yace daddy ni ba yanzon ba.


 sai yaushe?


 daddy idan na shirya zanyi mgn


cikin fada daddy yace baka isaba rana daya zakuyi aure KO kaki KO kaso kanajina?


daga kai yayi sannan yace daddy inason zamuyi mgn amman su taslim su fita tukum



🕊🕊

Mmn Yazeed

           🕊🕊🕊

[10:02PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

         🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*




*Gaisuwa ta mussaman gareku*

_matar abbatie barno_

    _hussaina faji_

      _murjanatu_

       _yahancy_

         _hajju_

             &

         _zinat_

*all in Fadeela Lamido novels group*



24 - 26



Daddy ne ya umarci su taslim da fatima da su fita

 

 bayan sun fita daddy  yace toh inajinka.


  saida haydar yayi kasa da murya sannan yace daddy dama shawara zan bada yariyar nan fa be kamata salis ya aure ta ba, dan sai da ta gama yawon ta tukun aka kawo ta gidan nan.

  

  da mamaki daddy da ummi suke kallon           haydar 


 daddy yace a ina kaji wannan lbrn ?


 kanshi tsaye yace yadidko ce ta fadamin


   sai alokacin salis ya dago kai ya kalli haydar


  daddy yace hjyr da kanta ta fada maka haka, toh gaskiya bahaka lbrn yake ba kuma ko ba ayi haka ba dama zangawa salis halin da fatima take ciki sannan yajuya barayin ummi yace ke dama tun zuwan fatima gidan nan nafada miki halin da take ciki.


   kai kuma haydar karna sakejin wannan kallamar abakin ka fatima bata yawo fayd'e aka mata shine dalilin da mahaifiyarta ta kawota.


  kan salis na kasa har yanzun be dago ba hawaye ne kawai ke zubo masa.


  ganin halinda salis ya shiga daddy yace wa haydar tashi ka tafi.


mikewa yayi yana kallon salis yana mai farin cikin yau ya dana tarkon shi adai dai.


   yana fita daddy ya mike ya taho kusa da salis hannun shi yasa ya dago kansa ganin fuskar yayi tajike sharkaf da hawaye ahankali ya fara sharemai hawayen sannan yace kayi hakuri babana kar kace wannan abun zaisa ka fasa abinda kayi niya inason ka yadda da kaddara mekyau da mara kyau wannan abinda ya faru da fatima zai  iya faruwa DA kanwar ka taslima kuma baza mu so taki aurowa ba saboda wannan dalilin, dan haka ka daure, 


  bece komiba ya mike ummi tace kuma duk abinda haydar zai fada maka karka saurareshi dan na kula so yake ya lalata mgnr.


   daker ya bude baki yace toh


   yana fita falo yaga wata yariya ta shigo

 riga da wando ne jikin ta sunyi matukar matseta cikin mamaki yace lfy wa kk nema.


  cikin hausarta wacce bata fita tace dan Allah Ina Neman haydar ne


  bece mata komi ba ya yamutsa baki ya shiga daki, yana shiga yacewa haydar kayi bakuwa kaje ka sallameta tunkafin ummi ta fito.


  atsorece haydar ya fito yana fadi axuciyar shi wacci yar iskar ce zata Jamai masifa


  yana fita sukai arba da ita, wata budurwar shice wacci suka kwashe kusan shekara biyu basu hadu ba suna hada idon suka sakar wa junan su murmushi cikkin sauri ya kamo hannun tasuka fita


salis na lekensu ta window har suka fita sannan ya koma kankujera ya zauna yayi tagumi yana bakincin wannan abu dazai ga wanda yayiwa zahara wanna abu lallai bazasu rabu lfy ba, daren ranar kasa bacci yayi haydar kuwa tunda ya fita sai 7:33am ya dawo lokacin salis ya fito wanka yana kokarin saka riga.


  yana shigowa ya fara fadin angon fatima meye lbr kodai haryanzon kana kan bakar ka .

 

banza yayi dashi ya dauki key din motar sa yayi waje


  haydar ko bayan yayi wanka yau be nufi office ba, gidan su wata budurwar shi yaje ya daukota yakaita dakin anas.


  ad'akin ya wuni da mubaraka saidare ya maidata gida har ya kama hanyar gida yaji shifa har yanzun hakalin shi be kwanta ba so yake ya sake kasan cewa da wata nan ya fara tunanin wacce yariya zai d'ako wadda zata kwantar mai da sha,awar shi.


  tunani ya fara yi cikin yan matan shi wad'an da yake harka dasu wan da besan yawan suba dan sufi dozin, kasa tuna ko guda daya yayi sai dai abinda ya bashi mamaki daya fara tunanin girjin fatima yake gani lokacin da takewa salis shagwaba, lashe baki yayi sannan yace inama nine salis na samu damar da yariyar nan takema wannan girgiza kasa daina tunanin fatima yayi dan haka daganan ya wuce mashayar su yasha yayi tatil besabo komawa gida aranar ba sai washe gari.


 damuwa ya taro yayiwa salis yawa abin duni ya isheshi yau haydar kwana biyu kenan be kwana gida ba yana cikin tunanin nan wayar shi tayi kara yana dubawa yaga anas ne abokin haydar da sauri ya dauka cikin faduwan gaba yace anas ina haydar.


  daga cen cikin wayar aka bashi amsa gayin nan dama nakiraka ne kazo ka shiga dashi cikin gida bayajin dadi ne, cikin sauri yadar ya mike ya fita.


  ganin haydar yayi rike ahannun anas idon shi rufe, yana isa gurin warin giya ya daki hancin shi.

ja yayi da baya daidai lokacin hancin motar daddy ta sawo kai cikin sauri salis ya kama haydar yana kokarin barin wajen dashi, amman ina tuni daddy ya karaso guri yana fadin lfy meya sameshi, salis kasa mgn yayi anas ne yace beda lfy ne


 daddy na isa gaban haydar yace innalillahi wa inna ilaihir raju,un haydar dama abinda kake kenan .


  juyar da kallon shi yayi gurin anas yace kamayar dashi inda ka dauko shi nabar makushi kar ya Kara dakowa inda nake na yafeshi acikin 'ya'yana.


  salis yace dan Allah daddy kayi mai hakuri.


   kai salis babu abinda ya dameka dan haka maza ka shiga gida, Ku kuma Ku fitar min agida


juyawa yayi yana waiwayen dan uwan shi har ya shiga gida.


  shiko haydar sai dare hakalin shi ya dawo jikin shi anas ya shiga fadamai abinda ya faru.


 tashin hankali ya shiga sosai nan da nan ya mike ko sallama bema anas ba.


  gidan alhj yusuf ya nufa ya sameshi zaune yana duba wasu takarddu


  alhj yusuf yaji mamakin ganin haydar acikin daren nan dan basu cika zuwa gidan shiba sabo da ba mata gareshi ba binshi yayi da kallo sanan yace kai kuma daga Ina?


   cikin rawar murya yace baba dan Allah ka taimakeni muje kaba Abba hakuri cewa yayi wai Karna kara shigo mishi gida.


   atakaice alhj yusuf yace me ka masa?


   kasa magana yayi sai hawayene keta zuba afuskar shi.


alhj yusuf ya sake cewa haydar me yasa bakajin maga ne ,alhj ya dade yana fadamin bakajin mgn kana mutukar bata mishi rai, jiya ya gama cemin wata ranama baka kwana agida, haka ne?


dukar dakan sa yayi kasa bece komai ba.


  shima shiru yayi yana kallon haydar  zuwacen yace tashi muje 


   bayan sun isa gidan atare suka fito daga cikin motar alhj yusuf ya dafa haydar yace haydar ko dai aure kk so?


dasauri ya girgiza kai.

 murmushi alhj yayi sannan suka shiga har falon daddy 


  daddy na ganin su ya mike cikin fada yace


 meyasa ka shigon min da wannan mashayin cikin gidana.


alhj yusuf yajuya ya kalli haydar yace mashayi kuma.


  eh katon mashayi ne ka tambaye shi giya yake sha.


  tsayawa alhj yayi shiru daga bisani ya dawo da kallon shi gasu taslim, yace kai ku tashi ku fita, ya juya ya kalli haydar yace kaima jeka dakin Ku.


  suna fita alhj yace yaya ni inaganin koran haydar bashi bane mafita ai sai abin ya kara lalacewa addu,a zamuyi tayi Allah ya shiryeshi, kuma ni Ina ganin yakamata amai aure kila ta sanadin haka saikaga ya shiryu, haka yayita wa daddy nasiha cikin dabara har ya saki jiki suna hira.


 bayan kwana biyu salis ne zaune shi da fatima ababban falon gidan suna hira kallon shi fatima tayi ta d'a hannunta tanuna mai yaya wai bakaga nayi lalle bane,


   nagani Zahara yayi kyau sosai amman ni banason kinayi ki bari sai munyi aure, kinga kayan nan ma na jikin ki da zakiji mgn ta danace ki daina sawa idan kuma zaki saka toh ki daura hijjab akai.


  turo baki tayi sannan tace waikai badama nayi ma kwalliya saika gwale ni.

   murmushi yayi sannan yace bahaka bane zahara nagani kuma ya burgeni.


   cikin muryan kuka tace toh ai baka kallaba.


  ahakali ya mika hannun shi ya rike nata duk 2 yana kallon su ,zuwa cen yayi ajiyar zuciya cikin muryar rada yace zahara. dagowa tayi da sauri ta kalleshi cikin ido. yace hannunki laushi.


  da sauri ta kwace hannunta tana rufe ido.


ahankali ya sake cewa zahara zaki iya gane mutumin da ya keta miki mutuncinki?

   gabanta ne ya fadi dan bata taba zatan salis yasan wannan mgn ba .


   muryar haydar sukkaji daga bayan su yana fadin toh iidan kasan shi me zaka mai?


   cikin sauri sukka kalli gurin haydar ne tsaye  hannun shi cikin aljjihun shi.


   salis ya bude baki zayi mgn aka turo kofar falon ,wata budurwa ce agaba bayanta kuma wata matace dagani mahaifiyar yariyar ce


  suna hada ido da haydar ya zaro ido yace me kika zo yi agidan mu?


    babu ko alamar tsoro atattare da ita tace niba gurinka nazo ba, nazo ne ingayawa iyayen ka ina dauke da cikin ka



  

🕊🕊

Mmn Yazeed

            🕊🕊🕊

[10:02PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*




27 -29




Da sauri ya farajan yariyar yana kokarin barin gidan da ita ummi ce taji hayaniya yayi yawa da sauri ta fito, ganin haydar najan yariyar ta fara dakamai tsawa cikin sauri ya saki yariyar yana mazurai, ummi takalli dadtijuwar matar da suke tare da yariyar tace sannu da zuwa hajiya shigo ki zauna.


  ba musu tahau kujjera ta zauna fatima da salis ko kallo sukabi yariyar dashi.


  haydar ko yana jingine jikin bango sai aikawa yariyar harara take


 ummi ce taji shirun yayi yawa tace baiyawar Allah ban fah ganeki ba.


  kamar jira matar take tace dama ai bazaki gane ni ba amman ai d'aki haydar bazai ce be gane mu ba,  atakai ce dai hajiya Nazo ne na shaida miki 'yata zinat ta dauke da cikin danku haydar



wani zufa me dumi ya karyo ma ummi take ta Fara fadin innalillahi wa Inna ilaihir raju,un maimaitawa taitayi zuwa cen ta daga jajayen idonta ta kalli haydar kanshi akasa yace ummi nifa karya suke min.


 bata ce komaiba ta mayar da kanta kasa wasu hawaye ne masu dumi suka zubu mata zuwa cen ta miki ta nufi falon alhj salis ne yabi bayan ta yana fadin ummi karki gayamai Dan Allah .


 waigowa tayi tace salis wannan ba abun da za,abuye bane , dole ne yasan halin da haydar yake ciki dan ni yanzon ban san yadda zanyi da wad'an nan mutane ba, tana fadin haka ta shige dakin.


   bata dade ba saiga su sunfito tare da daddy yana huce.


   fatima naganin fitowan daddy tamike ta nufi dakin su cike da tsananin tsanar haydar azuciyar ta.


    daddy ko kallon haydar yayi cike da bacin rai sannan ya juya ya kalli bakin nasu  sannan yace kai haydar fita kabar min gida, ku kuma kutashi ku bishi karku kara gigin nufumin gida da nufin Ku kawo min shege bazan taba karba ba.


   haydar ne ya bude baki yace daddy nifa karya suke min.


idan kasakemin Wata mgn zan illataka ka fita kabar min gida wai gawa yayi barayin matar cikin tsawa yace kutashi ku bishi, cikin rawar jiki suka mike suka fita dan tuni haydar ya fita salis ma mikewa yayi zaibi bayan su 

 daddy yace karka fita tsayawa yayi ya jingina kanshi ajikin bango.


 ummi ko kuka take yi tana fadin alhj wannan hukunci beyi ba, matar tabani tausayi be kamata amata hakaba ,yanzon yaya zatayi kenan?


  Oho nidai bazan karbi shegeba d'an karamin shi dashi ya lalata rayuwuwar shi, yace na mashi aure ne ban mashi ba? wacce irin jaraba ce wannan yariyar nan ma ai inbanda jaraba ta girmeshi haka daddy yayita fada wata mgnr ma besanin sanda ta fito bakin shi.


 ummi ko kuka take sosai yayin DA salis ke tsaye jikin bango


haydar ko yana fita ko waiwaye babu ya nufi motar shi shiga yayi ya zauna daidai lokacin zinat da mamarta suka fito harara ya wurgawa Zinat itama ta mayar da nata hararan motar shi yaja yabar wajen.


 yana fita agidan ya fara kuka hawaye ne yake zubomai kaman karamin yaro yana bakin cikin batawa iyayen shi rai da yakeyi amman ya kasa cen zawa, tsawa yayi bakin hanya yayi kuka sosai sannan ya kama hanyar gidan alhj yusuf.


 alhj yusuf naganin haydar gabanshi ya fadi sakamako idanuwan shi dasuka kunbura tahowa yayi ya kamashi ya zaunar dashi ya fara tambayan shi me ya faru amman ina haydar babu baki domin kuwa ya kasa cewa komai illah hawaye dake bin kuncin shi.


alhj yusuf ne ya lura haydar bazaiyi mgn ba, dan haka ya daga waya ya kira daddy.



  daddy na daukan waya yace au gurin ka ya taho, toh maza ka ko reshi karka sake kabar shi a gidan ka mazinaci ne dan iska .


 takaicine ya kama alhj yusuf yace yanzo yaya dan daka haifa kake kira da wad'an nan mugayan kalamen.


ba d'ana bane ayan zun tunda yace shi d'an iskane na barma duniya kuma kaima karka kuskura ka tareni da mgnr haydar yana fadan haka ya katse wayar.


  alhj yusuf ya sauke wayar ya kalli haydar yaga har yanzon hawaye ne a idon sa kamar anbude fanfu


ya mayar da kanshi kasa zuwa cen ya d'ago ya kalli haydar sannan yace haydar aure za,amaka kuma ba ina neman amincewan ka bane za ayi auren ne ko kana so ko baka so.


   *Kuyi hakuri yau banyi typing da yawa ba insha Allahu gobe zanyi me yawa*


🕊🕊

Mmn Yazeed

            🕊🕊🕊

[10:02PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*



30 - 32



Bece komai ba har yanzon kuka yake yana mamakin zinat anya kuwa ba karya suka shirya mai ba domin shi rabon daya ganta ya dade kuma ai bakai tsaye yake shigarta ba.


  kwanan haydar 2 agidan alhj yusuf zuwa yanzon ya dan saki jikin shi saidai ya dan rame gashi zama agidan ya isheshi dan alhj yusuf ba mata gareshi ba, dan haka gidan babu dadin zama.


 shima alhj yusuf zaman ya isheshi Dan haka ya fara tunanin dawo da salame saidai be saniba ko haryanzo iyayen nashi nanan akan bakan su.


  washegari yanufi gidan dada sallama yayi ya shiga dada ta tareshi da Fara,a itako salamatu tana ganin shi ta shige daki bayan sun gaisa da dada shiru sukayi nadan wani lokaci sannan alhj yusuf ya fara fadawa dada kudurin sa.


 farin cikine ya rufeta har ta kasa boye murnanta daki ta shiga cikin farin ciki amman saita tarar da salamatu tana kuka.


 tana ganin dada tace dada nifa bazan koma gidan sa ba, shekarana uku da dawowa garin nan betaba lekomuba tunda ya karbi yarshi sau 1 ya barta tazo gidan nan be mason tayi alaka dani sabo da ayanzo bana gaban shi dan haka ni bazan saurareshi ba.


 fada dada ta fara tana fadin wani irin tunani ne wannan da baki gabanshi aida bezo gidan nan da niyar zai maidaki dakin kiba kikasan dalilin shi nayin haka ki tunafah tunda ya rabu dake haryau beyi aure ba dayake ke butulu ce har kk wannan mgnr toh tashi maza kije ki saurareshi .


koda alhj yusuf yayiwa salamatu bayani batace a,aba aman fuskar ta adaure take tam kamar bata dariya dan haka hankalin alhj yusuf ya tashi yace salamatu kodai yanzon baki ra,ayi nane?


cikin fushi ta fara zaiyanane mishi kamar yadda ta fadawa dada.


farin ciki ne ya kamashi ashe har yanzon yana nan makale azuciyar ta yana murmushi yace Allah ya huce zuciyar ki nayi kuskure kuma ina neman afuwarki ki yafemin kuma idai fatima ce harsai kin haji da ganin ta haka alhj yusuf yayita rarrashi salamtu harta yadda ta amince sannan ya fada Mata shifa baya son abun ya dau lokaci dan haka suka tsaida akan ranar juma,a me zuwa.


yana barin gidan gidan mahaifin sa ya nufa ya fada masa kudurin sa.


 murnace ta kamasu gaba daya har yadidko godiya sukayiwa Allah tare dayiwa dansu fatan alheri.


   *Ranar juma,a*


taslima da fatima zaune adakin su suna hira taslim tace wlh fatima na kosa atsaida ranar bikin ku.


  tsaki fatima tayi sannan tace


  nidai gaskiya ban kosa ba keni idan ma naji anyi maganar bikin gabana fadowa yake shima yaya kullu maganar shikenan wai ya kosa ranan nan fah har cewa yayi zai gayawa daddy, waishi hakurin shi ya fara karewa



tintserewa tayi da dariya sannan tace ai yadai fad'amiki ne amman ba iyawa zayiba , da dai yaya haydar ne, sake kallonta tayi sannan tace yauwa sister naga wani abu acikin akwatin ki acikin wani d'an karamin akwati.


 "murmushi fatima tayi sannan tace eh yaya ne ya bani"


" taslim ta sake cewa menene aciki?


dafata fatima tayi sannan tace kai taslim kin cika gulma toh nima bansan menene aciki ba kuma yace karna bude sai ranar da akadaura mana aure.


 cafdi ai inda nice wlh saina bude yasan..........


 gud'an da ummi ke rangad'awa ne ya dakatar dasu daga hiran mikewa sukayi atare suka fito suna rige rigen tambayan ummi .


cikin farin ciki ta dafa fatima tace 

 fatima ki godewa Allah yanzon haka mahaifiyar ki tana gidan babanki an mayar da auren su, yazon salis yayi waya yace gashima agidan.


wani farinci ne ya kama fatima ta saki murmushi zuwacen kuma ta fashe da kuka.


ummi ce ta kamota ta rugume tana fadin haba fatima keda zaki godewa Allah kuma, meye na kuka .


  saidare salis ya dawo hannun shi rike da ledoji bayan yayi wa ummi sannu da gida ya kalli taslim yace ke Ina zahara?


 kallon shi tayi sannan tace tana  daki, yaya wai meye acikin ledar?


   "yana tafiya yake fadin inaruwan ki"


washegari


salis ne ya dauki taslim da fatima zai kaisu gidan alhj yusuf murna ce ba kadan ba azuciyar fatima.


 suna shiga gidan suka samu haydar kwace akan kujera yana danna wayar shi salis ne ya nufi gurin shi ya kama kafafuwan shi ya d'aga sannan ya zauna agurin tsaki haydar yaja sannan ya tashi ya zauna salis ne yace wa haydar ina mama?


  atakaice yace tana ciki.

  daidai lokacin  salamatu ta fito daga daki fatima ta tashi da sauri ta nufe ta, tureta tayi ta jawo taslim dake bayanta ta rungume sannan tacewa fatima aike babu ruwana dake.


komawa tayi kusa da salis ta zauna tana turo baki.


 kallonta kawai salis yayi ya sunkuwar dakai.


  mama ko tana rungume da taslim tana tambayan ta karatun ta.


 alhj yusuf ne yayi sallama ya shigo zama yayi cikin su bayan sun gaisa ya tashi ya nufi d'aki


 itama mama mikewa tayi sanna tacewa taslim tashi ki shiga kitchen ki debo muku abinci, tana fad'an haka tashiga d'aki


  haydar ko sai, satan hararar fatima Yake


  salis ko kallon fatima yayi yace ke wai baki iya bada hakuri bane?


 kara turo baki tayi sannan ta kauda Kai, daidai lokacin taslim ta kawo abinci ta ajewa salis nashi sannan tacewa fatima sister zo muci.


  azuciye tace banzanci ba.


" har salis yakai abincin dafda bakinsa yadawo dashi sannan ya kalli fatima yace sabo dame bazakici ba?


saida ta kara turo baki sannan tace toh aini batace dani ba kuma saina kamaci sai kace mayya.


dariyace taso kubucewa haydar amman sai ya dake yaci gaba da danna wayar shi.


  salis ma dakewa yayi sannan yace toh ke wai baki iya bada hakuri bane, kitashi maza tun kafin raina ya baci kije ki bata hakuri.


   mikewa tayi ta fara kuka tana buga kafarta akasa kamar karamar yariya tana fadin nifah ba abinda na mata ni yaushe ma naganta bare na mata wani abu.


  tun salis na kallon fatima har ya gaji ya rufe idonshi dan ya lura yau fatima so take ta rud'ashi.


   shiko haydar baki ya saki yana kallon fatima tuni yanayin shi ya fara cenzawa ji yake kamar ya tashi ya rungume ta


  fatima ce ta lura haydar ita yake kallo dan haka ta tsaya cak tana mamakin shi kuma wannan me yake kallo.


  salis ko yanajin fatima ta daina kuka ya bude ido cikin bacin rai yace meyasa kike min haka ne zahara dan Allah idai baso kk kijamin fushin Allah ba toh ki dakata da irin wannan abun, kije kiyiwa mama sallama kizo mutafi.


   sumi sumi ta wuce ta tura dakin mama tana shiga haydar ya kalli salis yace wlh kai wawane d'an kauye.


 murmushi salis yayi tare da mikewa yana fadin Allah ya shirye ka.


  zuwacen mama da alhj yusuf suka fito fatima na rike hannun babanta .


alhj yusuf yaga salis da taslim tseye yace kardai har zaku wuce?


  salis ne yabashi amsa eh baba zamu tafi.


  yace toh daman Ina son ganinku kaida haydar tsakanin ku wanene akace sun daidaita da fatima?


da sauri haydar ya d'akai ya kalli salis shima salis d'in kallon shi yayi


 🕊🕊

Mmn Yazeed

            🕊🕊🕊

[10:02PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*



33-37



Alama salis yakewa haydar ya fad'a aman haydar sai make kafad'a yakeyi.


 alhj yusuf yace daku nake mgn fa .


  " taslim ce ta lura salis kunya yakeji dan haka tayi sauri tace baba yaya salis ne.


haidar ne ya d'ago kai ya harari taslim yace ke dan ubanki dake ake mgn


  alhj yusuf yace haydar me yasa bakin ka ya iya furta zagi ne, ai taslim batayi laifi ba abin da tayi kai ya kamata ace kayi amman sai kayi shiru, juyawa yayi ya kalli salis yaga ya dukar dakai yace salis ni dama nasani baban ku ya fad'amin dama naso ne naji daga gareku amman tunda kun kasa magana taslim ta fanshe ku.


   ya juya ya kalli haydar yace toh kai kuma fah.


  baba ni bayanzon zanyi aure ba .


    bata rai baba yayi yace toh sai yaushe?


   idan salis yayi ni daga baya zanyi.


  baka isaba kafison kai ta d'ako mana mgn ai ni inda sosamu ne nan da one week kayi aure dan haka duk abinda akeci nan da Wata 1 kawo yariyar da kk so,Dan mun riga mun yake rana nan da wata biyu dan haka kuje kufara shiri.


haka suka koma gida cike da farin cike sai dai azuciyar salis ranar da akasa yayi mai yawa

 dan haka da suka kebe da fatima yace zahara gaskiya ranar nan da akasa yayi yawa.


 haba yaya wata 2 ne yayi yawa toh ni wlh kusa ma naga yayi min dan nifah wlh tsoron ma ranar nakeji.


 da sauri ya kalleta tsoro kuma toh tsoron me kikeji, kardai ki kecemin tsoron miji kike, toh idai haka ne gara ma tun yanzon ki cire shi dan gaskiya bazaki takurani ba , zahara kinsan fan nayi hakuri


  haharara shi tayi sannan tace hakuri me kayi?


   murmushi yayi sannan yace Zahara Kenan kisan fah kina da kyau kuma na kusa najiki jiki na


kawai daurewa nakeyi karne abin kunya, kasa ya yayi da murya ya Kira sunanta sannan yace kifah shirya dan idan mukayi aure akan kirjin ki Zan rinqa kwana.


 hannuta tasa ta rufe ido dan be saba mata irin wannan maganganun ba.


  murmushi yayi sannan yace zahara idan akace yau andaura mana aure bakaramin farin ciki zanyi ba, bare kuma na ganki ad'akina, Hmmm ranar zan nuna miki irin son da nake miki zan tarairayeki kaman kwai zan nunamiki soyayyar daba kowane namiji bane zai iya nunawa matar sa irin saba.


 kwashewa fatima tayi da dariya sannan tace amman dai yaya sambatu kk KO, wannan irin cin buri ne haka.


  shima dariya yayi sannan yace aidama nasan bazaki gane ba amman ahankali zan ganar dake, mikewa yayi tare da fadin bari naje gurin haydar.


  dasauri tace bayan zon ,muka dawo ba shine har zaka koma, ni wlh natsani haydar d'in nan banason ganin shi.


  shima cikin mama ya kalleta yace zahara kinada hankali kuwa d'an uwan nawa, meya miki ?


 toh yaya ai shima ya tsane ni dan haka nima bana sonshi wlh ko sunan shi aka kira gaba na faduwa yakeyi.


 kallon ta yayi cikin ido yace xahara haydar ba tsanar ki yayi ba haka halinsa yake nima bakiga yana min ba, kuma dan Allah ki yafe masa karki kara kullatan shi aranki kinga d'an uwanki ne , koya miki wani abu kijin haushi toh ki gayamin ni kuma xan faranta miki rai kinji KO ?.

 

 da sauri ta d'aga kai .


  yace kin yafe masa?


  eh tace ahankali.


Shirye shiryen biki nata kankama acikin wannan family ummi shiri take sosai komai ta gama had'awa da  dan ganci na

 fatima dan yazun bikin saura sati 2 kuma har wannan lokacin salis be kawa yariyar da zai aura ba dan haka akabar batunsa dama alhj yusuf ne yaso ahad'a amman daddy tuni yabar zancen haydar kamar yadda yace ya cireshi acikin 'ya'yan shi.


  haydar ne zaune shida abokin sa  anas a harabar gidan su anas sigari kawai yake sha daya shanye wani sai ya kara d'akkowa 


  anas ne ya lura haydar ya kusa shanye kwalin sigarin dauke ragowar yayi sannan yace big boy waikai meke damun ka?


  yana fesar da hayakin dake bakin shi yana fadin fatima.


  Hmm daman aikai ya kamata ka aureta sai da fad'a maka kace bahaka ba sai yanzun da lokaci ya kure zakace wani fatima, kana nufin sonta kk?


 niba sonta nake ba amman ni banason salis ya aure ta, saboda Ina matukar sha,wan yariyar dan haka nafison wani daban ya aure ta, yanzun fah duk tarin 'yan matan dana ke dasu basa birgeni Dana rufe ido fatima nake gani


tsaki anas yayi cikin takaici yace toh yanzon dai saidai kayi hakuri garama ka cireta aranka dan tafi karfin ka.


  tsaki shima yayi yamike yabar wajen tundaga ranar haydar ya zama kamar mara lafiya baya mgn sosai besan me yake damun shiba.


  Yau sauran kwana biyu biki dan haka yan baki sun fara isowa fatima da taslim sai shirye shirye sukeyi  daddy na cikin farin ciki.


  ummi ce ad'aki zaune da kawayenta suna kallon akwati ta zuwa cen saiga salis rike da hannun haydar ummi ce ta kalli haydar tace meya kawoka?

  

 haydar ne yace ummi ninace yazo yaga akwati.


  cikin fad'a tace to tunda kai ka kirashi saika shirya amsan da zakaba babanku idan yadawo ya samu haydar agidan na, mikewa tayi tafita adakin ahankali mutane dake dakin suka fita daya bayan daya.


   haydar ya tsuguna gaban akwati yana dariya yana duba kayan zuwace yace brother kaya sunyi saidai kacika hijjab dayawa aciki.


  murmushi salis yayi sannan yace ra,ayina kenan.


  anagobe daurin aure da daddare salis ya shiga har d'akin su fatima fatima ya hango manne jikin gado ta rufe fuskarta gefe ko kawayen su ne zaune suna hira sunna ganin shigowan shi suka bar daki gaban Fatima yaje ya tsuguna dariya yayi sosai sannan yace zahara duk tsoron auren ne haka, 


  batace kome ba ya sake cewa  zahara dan Allah ki kwantar da hankali bana son ganinki cikin wannan halin .


cikin kuka tace yaya kwata kwata banajin dadi, azuciyata taki natsuwa nayi nayi in natsar da ita nakasa gani nake kamar wani abu zai faru.


  da sauri yace babu wani abu dazai faru zahara sai alheri kiyi tunani dakau kila akwai abinda yake damunki.


   shiru tayi zuwacen tace yaya jiya nayi mafarkin na auri yaya haydar.


  dariya yayi sannan yace ni daman nasan akwai abunda yake damunki dan Allah ki cire tsanar haydar azuciyar ki, kuma kidaina wannan tunanin mafarki ne kawai insha Allahu gobe warhaka burin mu ya cika saida muyi fatan cikawa da imani, haka haydar yayi ta rarrashin fatima harta fara dariya.


  washe gari aka tashi da shirye shiryen dauren aure tun 12:00 bakin daddy suka fara halara kofar gidan ya ciki makil da jama,a sai hada hada ake salis ne ya fito cikin babban riga farare kal yayi matukar kyau waige ya farayi yana neman haydar amman ko alamar shi begani ba dan haka ya shiga neman no barshi tsaki yaje sabo da layin kwata kwata yaki shiga ya koma cikin abokan sa ya tsaya ranshi bace  zucen yaga guri ya kara cika duba agogo yayi yaga karfe 12:43 cikin sauri ya nufi motar shi wani abokin sane yabi bayan sa yana fadin inakuma zaka?


  yana kokarin barin wajen yace tahir yanzon zandawo zanje na dauko haydar ne.


  gidasu anas ya nufa yana tura kofar anas dakin yaga haydar zaune ya tasa sigari cikin zafin zuciya yace haydar kana nufin bazaka halarci daurin aure na bane?


  bece komaiba dan haka yasa hannushi ya fara jawoshi bayan motar ya turashi anas ma ya shiga sun kamo hanya kenan kiran daddy ya shigo wayar salis cikin fada yace kana ina?

  yace daddy ganinan zuwa naje dako haydar n.......


  salatin dasu anas kiyine ya dakatar da shi yana d'ago kanshi yaga Wata babban mota ta nufosu salis yayi kokarin kaucewa amman Ina tuni motar ta fara watan gaririya akan titi.basu kara sani me ya faru ba

zucen haydar ya bude ido ganin shi yayi kwace cikin jini muryan salis yaji yana kiran sunan shi daker yaja kashi ya kalli gurin kwance yaganshi jini na bulbulowa ta cikin shi jan jiki ya fara har ya isa gaban shi ya kama hannun shi babu abun yake kira banda zahara zuwace yayi kalmar shada be kara motsawa ba  haydar ya farajan shi duk da shima ajikace yake.


  karan wata mota yaji yana kallon gurin yaga  daddy da baba yusuf suna tahowa, gurin salis suka nufa daddy ne ya daga hannun shi yace ya innalillahi wa inna ilaihir raju,un Allah ya karbi abun sa😭😭



🕊🕊🕊

[10:02PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*


*Gaisuwa da fatan alheri gare ku*


*Zainab bobbo adamawa*

*Yahancy gombe*  


*bilkisu muhammad*


   *xeeshata*


*mmn abdulnasir*


   *hajju lokoja*


       *Fatyma*


*harda wadan da bankira suna ba inajin dadin yadda kuke nuna sayayyar ku ga wannan lbr*😍😍😘


38 - 39




Tattara su akayi gaba daya aka nufa asibiti har anas.


  nan danan wannan mummunan lbr ya isa kofar gidan daddy dake cike da jama,a yan daurin aure.


  itako ummi daddy ne yamata waya ya gaya mata amman be gayamata rasuwan salis ba yadaice gasu sun wuce asibiti.


hakalinta ne yayi mummunan tashi dan ta dade tana munanen mafarkai akan salis da haydar


  itako fatima tun safe ta kulle kanta ad'aki tana kuka dan haka ummi tace abarta kar agaya mata abari aga abinda allah zaiyi.


  haka gidan ya zama jugun kowa da abin da yake sakawa.


  zuwacen daddy ya sake kiran ummi.


  tana ganin kiran daddy gabanta ya fadi tana dauka tace


  " alhj yaya abin da sauki kodai na taho ne kuna wanne asibiti?


  " cikin jarinta irin na maza yace basai kinzo ba muma gamunan tahowa kuma nasan ke musulma ce kin yadda da kaddara mekyau da marakyau.


kuka ta fara tace alhj kardai kacemin mutuwa sukayi?


  "a,a haydar yanan araye sai dai ya samu karaya acinya"


 kara rushewa tayi da kuka sannan tace salis fah ?


  cikin shashshekan kuka yace sai dai muyi hakuri hafsat salis ya koma ga mahalicin sa.


 ummi jitayi kafafuwan ta bazasu iya daukanta ba take ta yar da wayar ta shiga fadin innalillahi wa inna ilaihir raju,in.


  jin salatin da ummi keyi gaba daya hankalin mutane yadawo gurinta ummi tana kuka tana gaya musu salis ya rasu.


fatima dake kule ad'aki kunnen ta ya fara juyo mata koke koke da sauri ta bude kofar ta fito idon ta jajur bisu tayi da kallo daya bayan daya kowa afalon kuka yake.


  " cikin tsawa tace menene wani abu ne ya faru?


  Wata yayar ummi ce ta jawo ta jikinta nasiha ta shiga yimata sannan ta gaya mata rasuwan salis.


   jitayi kamar an buga mata guduma hawaye kuwa kamar an bude fanfu cikin kuka take fadin nashiga uku na lalace meyasa yayimin haka jiya fah  yace min yau tare zamu kwana shine kuma zai tafi ya barni kai ban yadda ba be mutu ba,nasan shi me cika alkawari ne.


   daidai lokacin daddy ya shigo mutane ne abayan sa dauke da gawar salis d'akin ummi aka shigar dashi da sauri fatima ta kutsa ta cikin mazan ta shige d'akin ,hannu tasa ta bude fukar shi girgizashi tayi tana kuka tana fadin yaya katashi dan Allah.


  daddy na tsaye abayan ta ya kasa cewa komai alhj yusuf ne ya d'agota yace fatima salis yariga ya tafi ki daina mai kuka soyayyar da zaki nunamai yanzun shine kibishi da addu,a


  wani hawaye ne me dumi ya zubo mata alhj yusuf najanta tana waiwayen gawar salis.


   bayan angama gyara salis aka kira ummi tamai addu,a cikin kuka tamai addu,a albarka ko tasamai babu adadi, daddy ne yace akira fatima suyi sallama.


  kamota akayi dan ayanZon bata iya tafiya saitin kunen shi taje babu meji metake cewa.


  daddy ne yoga abin nata bana kare bane dan haka yace afita da ita 


  haka sunaji suna gani aka tafi da salis gidan sa na gaskiya


  fatima ko mawa d'akin su tayi ta fashe da kuka kallon hannuta tayi taga zanen fulawa wani haushine ya kamata tunani yadda zatayi ta goge lallen ta fara 



dan haka ta fara buga hannun ta ajikin bango tuni kyawawan warwaro dake hannun ta suka lanlan kwashi.


  dada ce tahigo taga halin da Fatima take ciki da sauri ta riketa tana fadin meye haka fatima saikace ba musulma ba, dan Allah dan darajan annabi ki dainawa bawan Allah nan kuka.


 suna cikin haka salamatu mahaifiyar fatima ta shigo, fatima ta daga kai tace mama kin ga haydar ya kashe salis KO ?


  cikin tsawa mama tace waye yace miki haka, kifah dai na irin wannan surutun ki kama bakin ki, haydar d'in da kike mgn shima yana cen akwance bemasa inda yake ba.


  cikin kuka tace


  " ai dama bazai san inda yake ba kuma da ikon Allah shima mutuwa zaiyi"


  cikin zafin zuciya mama ta nufi gurin ta gadan gadan



🕊🕊

Mmn Yazeed

            🕊🕊🕊

[10:36AM, 3/31/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

  ( ta wuya ake kamashi)

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*




17-20




Taslim ce ta zaro ido dan tunda suke da haydar betaba kaita unguwa ba fatima ko idonta ne ya cika da hawaye dan ko muryar haydar taji sai cikinta ya murd'a



salis ya lura da halin da suka shiga ci dan haka yace haydar ai inaga kubar tafiyar nan sai gobe dan nalura zahara batajin dadi sosai 


 ysaki haydar yayi ya bar wajen.


   da dadare anas ya kawowa haydar ziyara har dakin ummi yaje ya gaisheta domin shi ba bako bane agidan adakin ya samu salis dan haka ya dan zauna suna hira bayan sundan taba hira anas ya nufi dakin su haydar 


  hira suka barke acikin hiran tasune haydar yake cewa anas akwai wata yariyar kanin daddy da ta dawo gidan nan tana min kama da yariyar nan da na huta da ita a wannan kauyen.


 dariya anas yayi sannan yace kace dai yariyar nan tasamu matsayi tunda gashi har gizo take maka


  yatsuna fuska yayi sannan yace bahaka bane anas kaima nasan idan ka ganta zaka gane tsananin kamar su.


  suna cikin haka taslim tashigo da kula ahanun ta ta ajiye agaban anas tace gashi injji ummi.


  hayadar yace ke ina wannan yariyar ?


 wacece fatima?


  tsawa ya daka mata  dan ubanki ina tambayanki kina tambaya na, koni sa,an wasanki ne


yamusha fuska tayi sannan tace toh ai ban gane wacce kake mgn bane idan fatima ce tana dakin ummi.


  atakai ce yace jeki kirata


zuwa cen saigata ta shigo tare da sallama tsugunawa tayi akasa dan balakin tsoron haydar take ta bude baki ahankali tace yaya haydar taslim tace kana kirana.


be dago ya kalleta ba cigaba yayi da danna wayar shi cikin kasaita ya bude baki yace ke baki ganin bakone bazaki gaida shiba nifa ba salis bane wlh saina zaneki dan ni bana daukan raini.


  shikuwa anas har yanzon be kalle fatima ba illa cin abincin da yake dan haka lokacin data gaida shi ya dago kai ya kalleta.


  sakin abincin yayi ya fadi kasa ya mike da sauri


  ganin inda anas ya rude yasa shi yace ke tafi kiba ni guri


 tana fita anas yace wlh itace kai anya kuwa yariyar nan ba aljana bace.


  musu suka fara haydar na fadin kamace yayin da anas yace itace.


  ganin da anas yayi musun yaki karewa sai ya bude wayar shi ya bude hoton da ya dauki yariyar lokacin tana kwace amotar haydar zuwa yayi daf da haydar yanuna mai photo.


   karban wayar yayi ya shiga kallon hoton, wayar shi ya jawo ya tura sannan yayi delete na wayar anas cikin tashin hakali yace zanyi bincike akanta.


     shiru sukayi gaba dayan su kowa da abinda yake sakawa.


  aranan haydar yaje gurin kakar su yadidko tsayawa yayi ahanya yasai mata lemo dan yasan idan tana shan Orange saitai zuba zance.


 murna tayi sosai daganin haydar da kansa ya yanka mata lemon ta fara sha tana zubo masa wani lbrn daban .


   yana ganin haka ya fara saita mata hanya niba wannan ba hajiya nifa gaskiya fatima na bani tausayi ace yariya kamarta tana jss1 waisu toh garin su ba asa yara makaranta ne?


   cikin takaici tace ai bari kawai haydar baban ta ma yana bakin cikin wannan abu amma ai uwarta ce sula haka kawai ta dauki yariya ta kaita kauyen kayayau ko mota bata iya shiga.


   daukan wani lomon yayi yamika mata sannan yace kina nufin kauyen babu mota.


   saidata matsa ruwan lemon abakin ta sannan tace inafah suka ganta ai wanda ma ya keta mata mutuncin ta badan garin bane dan ita saima allokacin tasan sunan mota nandai ta kwashe komai ta gayawa haydar.


   haka haydar ya baro gidan cike da tashin hankali, yana fadi azuciyar shi lallai nayi abin kuya yazon wani hali 

iyayen mu zasu shiga idan sukaji nine na aikata Wannan abun gashi yaji kakar tasu sai fadan mugayan kalamai take ga Wanda ya aikata ma jikarta wannan aika aika


gidan su anas ya nufa ya labarta masa cin matsanan cin tashin hankali ya mike yace 


    " toh yanzon sai ka aureta kawai haka shine abinda ya dace saida nace maka karka taba ta amman kakiji kaga da duk haka bata faru ba"


  cikin zafin zuciya haydar yace dallah gafara ina neman mafita kuma zakawo min wata magana daban banason irin wannan.


 toh shi kenan tonda bakason agayam gaskiya amman ni bazan kara zuwa gidan ku ba dan idan daddyn ku yasamu wannan lbr harni saina shiga ciki.


  aniyarka ta bika in Allah ya yadda daddy bazaiji wannan maganar ba kuma kai nifa bazanma bari taci gaba da zama agidan muba saina san haryar da zanbi tabar gindan nan wlh dama tunda naganta agidan mu naji natsaneta gashi naga salis kaman sonta yake yi amman nasan abinda zanyi.


   shiko anas kallo yabi haydar dashi yanason yaba abokin nashi shawara amman yasan yanzon sai su kwashi yan kallo dan haka yayi gum.


     *********


 bayan haydar ya koma gida dakin su ya nufa ya cire kayan dake jikinshi sannan ya dauki jallah biyar salis ya saka ya haye gado ya kunna sigari yana sha


  zuwacen salis ya shigo yakali hayadar yayi tsaki cikin takaici ya fara magana wato dan iskanci ma yanzon har adakin ma shan sigari kake toh wlh abun ya isa haka bazan iyaba zan fadawa daddy.


 

kashe sigarin yayi ya mike yaje har gaban salis sannan yace baka isa ka hanani shan sigari adakin nan ba kai Ina hanaka kayi wani abu dakin nan ne ? , abin da kaga dama kakeyi dan haka baka isaba wlh.


   toh naji ban isaba amman me yasa 

ka saka min daya daga cikin rigar da nake sallah da ita bayan kasan ni bashan sigari nake ba kuma ina kyamar me Shanta


  Kara matsowa yayi dafda shi yace


    " nasa din kayi abinda zakayi "


  ran salis ya bacci idon shi yayi jawur kallon haydar kawai yake zuwa cen yayi kwafa sannan yace wlh darajan ummi kake ci dan banason na tayar mata da hankali amman ba komai wata rana zanyi maganin kka


   yana fadin haka haydar ya kamo wuyar rigar shi yahada ya matse yace 


 " dan Allah idan kacika kai jarumi ne kayi maganina yau basai wata ranba"


  rufe ido salis yayi zuwacen yace sakeni.


   cikin daga murya yace bazan sakeka ba


  salis gani yayi haydar na neman kure shi dan haka yasa hannun shi ya hankad'a shi ya fadi kasa cikin sauri ya bar dakin.


   falon daddy ya nufa ranshi bace, aciki ya samu ummi bayan ya zauna ummi tace


   lfy kuwa yanzon ka fita kana dariya kuma naga kadawo ranka bace wani abu ya faru ne?


  a,a babu abinda ya faru ummi amman dai inason dan Allah araba mana daki nida haydar


  daddy ya dago da sauri ya kalli shi, sannan yace kunyi fada ne?


 kanshi akasa yace bahaka bane kawai dai nafison ne na zauna ni daya


  murmushi daddy yayi sannan ya daga waya ya kira haydar, ba adade ba saiga haydar ya shigo atsora ce dan yazaci ko salis ya fadi abinda ya faru ne .




    🕊🕊

Mmn Yazeed

             🕊🕊🕊

_©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

        🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*



*Gaisuwa ta musamman ga duk wanda yake cikin wannan group  *Farfazaz novels* _kunfi ko wani group comment da nuna soyayyar ku akan wannan lbr Tsuntsu me wayo inajin dadin kasan cewa daku_ 💃💃💃😘



21 - 23



Zama yayi nesa da salis kanshi akasa dan duk abin shi yana tsoron daddy shi ahankali yace gani.


  daddy ya dago ya kalleshi yasa hannu ya cire gilas din dake idon shi sannan yace me ya had'a ku ?

  

  d'ago kai yayi ya kalli salis ya sake mayar da kanshi kasa yayi shiru.


 ummi tace wai ba dakai ake mgn ba ne


  bece komai ba kuma har yanzo kansa na kasa.


  daddy yace kyale su tun da bazasu fada ba ai sunfi kusa, amman nasan haydar ne baidan gsky wata kila ka kule shi ne amman ni araina banason kuraba daki nafiso sai kunyi aure kowa ya samu abokiyar zama ko ya kuka gani?


   haydar ne ya fara magana daddy ai ko munyi aure gida daya zamu zauna.


  cikin sauri salis yace dawa dakai Allah ya kiyaye wlh ba zan zauna dakai ba.


  sakin baki haydar yayi yana kallon salis sannan yace salis nine fah.


 fuskar salis adaure yace kaidin fah ina hauka ne zan zauna dakai.


  daga daddy har ummi basuji dadin maganar salis ba, 


 ummi ta juyo da kallon ta gurin salis tace 


 " ni bansan ka da fushi haka ba banji dadin mgnr ka ba idan baka zauna da dan uwan kaba dawa zaka zauna banajin dadin ganin ku cikin wannan halin dan Allah ku zauna lfy.


  juyawa tayi gurin haydar ta harareshi sannan tace kai kuma kabashi hakuri dan nasan kaine mara gaskiya.


   ahankali yace kayi hakuri in Allah ya yarda bazan kara ba.


  har yanzon fuskar salis adaure take dan haka daddy ya kira su gaban shi kama hannun su yayi ya hada yace ya wuce kutashi ku tafi.


  suna rike da hannun juna suka fita.


  ummi ta dawo da kallonta gurin daddy sannan tace


   " salis akwai hakuri amman idan ransa ya baci be iya fushi ba shiko haydar idan be nemi fitana ba bayajin dadi.


  ajiyar zuciya daddy yayi sannan yace Allah ya shirye su.


  haka rayuwa taci gaba da kasancewa agidan alhj kasim tsakanin salis da haydar yau ayi fada gobe ashirya zuwa anjjima  kaga kamar basune suka yi ba.


  kwanci tashi ba wuya wajan Allah dan yanzon kusan shekara fatima uku aku agidan, zuwa wannan lokacin shakuwa ce me karfe tsakanin fatima da salis.


 yayin da haydar ya hura wutar kiyayar fatima azuciyar shi dan ko mgn bata hadasu da ita


  duk da cewa ayanzon idan ka kalli fatima baza taba cewa tayi zaman kauye ba 


acin wad'an nan shekarun so daya babanta ya kaita gurin mahaifiyar ta yanzon  fatima tana ajin karshi na secondary sakamakon kwanya da Allah ya bata.


   ta bangaren ummi kuwa wato mahaifiyar su haydar bata nunawa fatima wani banbanci tsakanin ta dasu haydar dan haka tana cikin kwanciyar hankali matsalar ta daya haydar.


ayanzun dai fatima ta zama cikekiyar budurwa komai na jikin ta ya fito sosai 


  fatima ce kwace jikin kakarta yadidko tana danna waya yayin da taslim tana gefe tana cin abinci suna fira da taslim.


  sallaman alhj yusuf ya katsa musu hira, bayan yazaunaya kalli fatima  dake jikin mahaifiyar shi yace ke ashe baki da hankali katuwarki dake zaki kwanta mata ajiki, yajuya ya kalli taslim sannan yace ke kuma bakiyi mata fada.


  murmushi taslim tayi sannan tace baba tausa fah take mata.


  hararanta yayi sannan yace wai ma me kukeyi agidan nan yau kusan 3 days kenan inaganin ku anan ku koma gidan ku mana.


   taslim ce ta amasa munzo tayata zama ne ai yauma zamu wuce.


   yace gara dai kutafi hira sukaci gaba dayi shi da yadidko.


   zuwa cen su fatima suka fito cikin shirin ta fiya alhj yusuf ne ya kawosu har gida bayan sun gaisa da ummi ya wuce.


   washegari fatima nata zuba ido taga shigowar salis har wan 12 na rana bata ganshi ba dan haka ta shiga neman layin shi saida ta kira su uku ba adauka ba dan haka tashiga damuwa.


   lokacin da taslim ta kawo musu abincin rana kasa ci tayi tana juya cukalin.


  taslim tace sister wai meke damun ki tun jiya naga duk kinyi wani iri.


   meko ni bawani abunda yake damu na.


  taslim shiru tayi taci gaba da cin abincin ta.


  bayan sungama dakin ummi suka nufa suna shiga fatima tace


   ummi wai yaya salis baya nanne?


  eh bayanan bakuyi waya bane halan?


  tace nakirashi yaki dagawa.


ummi tayi murmushi tace kila baya kusa da wayar ne, munyi waya danzon yace min suna hanya.


   dariya taslim tayi tace dama shi yasa kika ki cin abinci wai ku soyayya kuke ne?


 fatima ce ta harari taslim sannan tace wani irin soyayya.


  ummi tace ke rabu da ita neman mgn ne da ita.


  dariya taslim ta sakeyi sannan tace wlh ummi soyayya sukeyi.


  daure fuska ummi tayi sannan tace wai taslim ina wasa dake ne nace kibar mgnr ina ruwanki da su.


  hannu tasa ta rufe bakinta sannan tace na bari ummi.


  daidai lokacin salis da haydar suka shigo bayan sun gaisa da ummi fatima gaida su haydar kadai ne ya amsa shima dan yaga ummi ne hakalin fatima ya kara tashi idonta ya cika da hawaye


 ummi ta lura da halin da fatima take ciki  bata dai ce komai ba dan bata faye son shiga tsakanin su ba


basu dade ba suka fita zuwa dakin su, fatima ko na gefe tayi tagumi.


   ummi ta juya ta kalleta tace


  fatima cire tagumin nan tashi maza ki kai musu abinci.


  har ta dauki abincin ta tuna salis beson ya ganta babu hijjab dan haka ta koma dakin ummi ta dauki hijjab ta fita.


 samun su tayi zaune haydar na nunawa salis wani abu acikin wayar shi sunata dariya aje abincin tayi tajuya har takai kofa haydar yace ke dauki ledar cen ki kaiwa ummi.


    dawowa tayi ta dauka ta fita, kafin takai dakin ummi hayawaye ya fara zubo mata saida ta share hawayen ta shiga dakin ummi ta aje ledar ta koma kusa da taslim ta zauna ummi ta bita da kallo batace komai ba ta mike ta fita.


 dakin su haydar ta shiga cikin mamaki

 suke kallonta.

    kallon salis tayi sannan tace waikai yaushe aka daura maka aure da fatima ne bansani ba


 da mamaki yace ummi bangane me kk nufiba.


 aidama bazaka gane ba kawai dan fatima ta tafi gidan hajiya bata fada makaba kk wannan fushin, matarka ce?


   da sauri ya girgiza Kai.

ummi ta sake cewa toh karage wadan nan dokokin takasa mata suyi yawa kuma kazo ka rarasheta


adakin su ya sameta tana kwance tayi rufda ciki ahankali ya kira sunan ta amsawa tayi batare data waigo ba ya sake cewa toh tashin mana.


   kintashi tayi dan batason yaga idon ta

  gaban gadon yaje ya zauna yace zahara tashi mana kosai nakira ummi ne?


tanajin ya kira sunan ummi ta miki ta fara sakkowa daga gadon binta yayi da kallo dan rabon da ya ganta babu hijjabi ya manta sai yaga ta kara kyau bayan ta zauna ya kalleta yace wato abin harda su kuka?


 cikin muryan kuka tace toh bakai bane kake fushi dani.


   cikin sauri yace nabari indai nine banason nasake ganin hawayen ki 


daidai lokacin haydar ya shigo dakin abakin kofa ya tsa dan haka salis ne kawai yaga shigowan shi


juyawa yayi barayin fatima yace tashi muje gurin ummi.


  tana mikewa yace toh kisa hijjab mana.


  buga kafa ta fara kamar karamar yarinya cikkin shagwaba tace ni gaskiya a,a nan da dakin ummi saina saka hiijjbi.


binta yayi da kallo zuwacen yayi murmushi yace ji abinda kikeyi saikace wata karamar yarinya 


  kara shagwabewa tayi 


   haydar ko dake bakin kofa tuni ya Fara rikicewa dan babu abinda yafi tayar mai da hankali kamar yaga mace tana wannan shagwaban, idon shi nakan kirjinta 


    salis kuwa ji yake kamar ya rungumita dan betabajin irin yanayin da yaji yau ba, juyawa yayi ya kalli haydar yace waikai wani gulman ne ya kawoka


    sai alokacin fatima tasan da shigowan haydar juyar da kallonta tayi gareshi 


  yace ke dena kallona munafuka kawai me suffar aljanu


  salis yakalleshi ya karasa gaban shi sannan  yace muje  


    *******

da daddare duk yan gidan ne suka hadu a falon daddy suna hira zuwa cen daddy yace mun kusa shan biki agidan nan.


   Ummita tace dama kuwa inason nama magana tunda su sunki yi .

 cikin sauri salis yamike zaibar wajen. alhj yace inakuma zaka dawo ka zauna 


  bayan yazauna daddy yace yakamata kuyi aure salis kaida nake ma ganin ka kamar me hankali.


  ummi tace alhaji ai haydar zakawa mgn shi yariga ya kama tashi gatanan kusa da kai duk da dai ba fada sukayi ba amman duk me hakali yasan sun amice da juna


   murna ce ta kama daddy yace toh shine ni baki sanar min ba


  dawai inajira ne su fada da bakin su gatanan ansa mata takunkumi zama da hijjab saikace matar liman 


  taslima ta kwashe da dariya shikuwa salis tunda ya dukar da kansa ya kasa dagowa fatima ma tana kudun dune cikin hajjabin ta


  daddy yajuyar da kallon shi ga haydar yace kaifah


  Sosa keya yayi sannan yace daddy ni ba yanzon ba.


 sai yaushe?


 daddy idan na shirya zanyi mgn


cikin fada daddy yace baka isaba rana daya zakuyi aure KO kaki KO kaso kanajina?


daga kai yayi sannan yace daddy inason zamuyi mgn amman su taslim su fita tukum



🕊🕊

Mmn Yazeed

           🕊🕊🕊


[8:17PM, 3/24/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

         🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*




*Gaisuwa ta mussaman gareku*

_matar abbatie barno_

    _hussaina faji_

      _murjanatu_

       _yahancy_

         _hajju_

             &

         _zinat_

*all in Fadeela Lamido novels group*



24 - 26



Daddy ne ya umarci su taslim da fatima da su fita

 

 bayan sun fita daddy  yace toh inajinka.


  saida haydar yayi kasa da murya sannan yace daddy dama shawara zan bada yariyar nan fa be kamata salis ya aure ta ba, dan sai da ta gama yawon ta tukun aka kawo ta gidan nan.

  

  da mamaki daddy da ummi suke kallon           haydar 


 daddy yace a ina kaji wannan lbrn ?


 kanshi tsaye yace yadidko ce ta fadamin


   sai alokacin salis ya dago kai ya kalli haydar


  daddy yace hjyr da kanta ta fada maka haka, toh gaskiya bahaka lbrn yake ba kuma ko ba ayi haka ba dama zangawa salis halin da fatima take ciki sannan yajuya barayin ummi yace ke dama tun zuwan fatima gidan nan nafada miki halin da take ciki.


   kai kuma haydar karna sakejin wannan kallamar abakin ka fatima bata yawo fayd'e aka mata shine dalilin da mahaifiyarta ta kawota.


  kan salis na kasa har yanzun be dago ba hawaye ne kawai ke zubo masa.


  ganin halinda salis ya shiga daddy yace wa haydar tashi ka tafi.


mikewa yayi yana kallon salis yana mai farin cikin yau ya dana tarkon shi adai dai.


   yana fita daddy ya mike ya taho kusa da salis hannun shi yasa ya dago kansa ganin fuskar yayi tajike sharkaf da hawaye ahankali ya fara sharemai hawayen sannan yace kayi hakuri babana kar kace wannan abun zaisa ka fasa abinda kayi niya inason ka yadda da kaddara mekyau da mara kyau wannan abinda ya faru da fatima zai  iya faruwa DA kanwar ka taslima kuma baza mu so taki aurowa ba saboda wannan dalilin, dan haka ka daure, 


  bece komiba ya mike ummi tace kuma duk abinda haydar zai fada maka karka saurareshi dan na kula so yake ya lalata mgnr.


   daker ya bude baki yace toh


   yana fita falo yaga wata yariya ta shigo

 riga da wando ne jikin ta sunyi matukar matseta cikin mamaki yace lfy wa kk nema.


  cikin hausarta wacce bata fita tace dan Allah Ina Neman haydar ne


  bece mata komi ba ya yamutsa baki ya shiga daki, yana shiga yacewa haydar kayi bakuwa kaje ka sallameta tunkafin ummi ta fito.


  atsorece haydar ya fito yana fadi axuciyar shi wacci yar iskar ce zata Jamai masifa


  yana fita sukai arba da ita, wata budurwar shice wacci suka kwashe kusan shekara biyu basu hadu ba suna hada idon suka sakar wa junan su murmushi cikkin sauri ya kamo hannun tasuka fita


salis na lekensu ta window har suka fita sannan ya koma kankujera ya zauna yayi tagumi yana bakincin wannan abu dazai ga wanda yayiwa zahara wanna abu lallai bazasu rabu lfy ba, daren ranar kasa bacci yayi haydar kuwa tunda ya fita sai 7:33am ya dawo lokacin salis ya fito wanka yana kokarin saka riga.


  yana shigowa ya fara fadin angon fatima meye lbr kodai haryanzon kana kan bakar ka .

 

banza yayi dashi ya dauki key din motar sa yayi waje


  haydar ko bayan yayi wanka yau be nufi office ba, gidan su wata budurwar shi yaje ya daukota yakaita dakin anas.


  ad'akin ya wuni da mubaraka saidare ya maidata gida har ya kama hanyar gida yaji shifa har yanzun hakalin shi be kwanta ba so yake ya sake kasan cewa da wata nan ya fara tunanin wacce yariya zai d'ako wadda zata kwantar mai da sha,awar shi.


  tunani ya fara yi cikin yan matan shi wad'an da yake harka dasu wan da besan yawan suba dan sufi dozin, kasa tuna ko guda daya yayi sai dai abinda ya bashi mamaki daya fara tunanin girjin fatima yake gani lokacin da takewa salis shagwaba, lashe baki yayi sannan yace inama nine salis na samu damar da yariyar nan takema wannan girgiza kasa daina tunanin fatima yayi dan haka daganan ya wuce mashayar su yasha yayi tatil besabo komawa gida aranar ba sai washe gari.


 damuwa ya taro yayiwa salis yawa abin duni ya isheshi yau haydar kwana biyu kenan be kwana gida ba yana cikin tunanin nan wayar shi tayi kara yana dubawa yaga anas ne abokin haydar da sauri ya dauka cikin faduwan gaba yace anas ina haydar.


  daga cen cikin wayar aka bashi amsa gayin nan dama nakiraka ne kazo ka shiga dashi cikin gida bayajin dadi ne, cikin sauri yadar ya mike ya fita.


  ganin haydar yayi rike ahannun anas idon shi rufe, yana isa gurin warin giya ya daki hancin shi.

ja yayi da baya daidai lokacin hancin motar daddy ta sawo kai cikin sauri salis ya kama haydar yana kokarin barin wajen dashi, amman ina tuni daddy ya karaso guri yana fadin lfy meya sameshi, salis kasa mgn yayi anas ne yace beda lfy ne


 daddy na isa gaban haydar yace innalillahi wa inna ilaihir raju,un haydar dama abinda kake kenan .


  juyar da kallon shi yayi gurin anas yace kamayar dashi inda ka dauko shi nabar makushi kar ya Kara dakowa inda nake na yafeshi acikin 'ya'yana.


  salis yace dan Allah daddy kayi mai hakuri.


   kai salis babu abinda ya dameka dan haka maza ka shiga gida, Ku kuma Ku fitar min agida


juyawa yayi yana waiwayen dan uwan shi har ya shiga gida.


  shiko haydar sai dare hakalin shi ya dawo jikin shi anas ya shiga fadamai abinda ya faru.


 tashin hankali ya shiga sosai nan da nan ya mike ko sallama bema anas ba.


  gidan alhj yusuf ya nufa ya sameshi zaune yana duba wasu takarddu


  alhj yusuf yaji mamakin ganin haydar acikin daren nan dan basu cika zuwa gidan shiba sabo da ba mata gareshi ba binshi yayi da kallo sanan yace kai kuma daga Ina?


   cikin rawar murya yace baba dan Allah ka taimakeni muje kaba Abba hakuri cewa yayi wai Karna kara shigo mishi gida.


   atakaice alhj yusuf yace me ka masa?


   kasa magana yayi sai hawayene keta zuba afuskar shi.


alhj yusuf ya sake cewa haydar me yasa bakajin maga ne ,alhj ya dade yana fadamin bakajin mgn kana mutukar bata mishi rai, jiya ya gama cemin wata ranama baka kwana agida, haka ne?


dukar dakan sa yayi kasa bece komai ba.


  shima shiru yayi yana kallon haydar  zuwacen yace tashi muje 


   bayan sun isa gidan atare suka fito daga cikin motar alhj yusuf ya dafa haydar yace haydar ko dai aure kk so?


dasauri ya girgiza kai.

 murmushi alhj yayi sannan suka shiga har falon daddy 


  daddy na ganin su ya mike cikin fada yace


 meyasa ka shigon min da wannan mashayin cikin gidana.


alhj yusuf yajuya ya kalli haydar yace mashayi kuma.


  eh katon mashayi ne ka tambaye shi giya yake sha.


  tsayawa alhj yayi shiru daga bisani ya dawo da kallon shi gasu taslim, yace kai ku tashi ku fita, ya juya ya kalli haydar yace kaima jeka dakin Ku.


  suna fita alhj yace yaya ni inaganin koran haydar bashi bane mafita ai sai abin ya kara lalacewa addu,a zamuyi tayi Allah ya shiryeshi, kuma ni Ina ganin yakamata amai aure kila ta sanadin haka saikaga ya shiryu, haka yayita wa daddy nasiha cikin dabara har ya saki jiki suna hira.


 bayan kwana biyu salis ne zaune shi da fatima ababban falon gidan suna hira kallon shi fatima tayi ta d'a hannunta tanuna mai yaya wai bakaga nayi lalle bane,


   nagani Zahara yayi kyau sosai amman ni banason kinayi ki bari sai munyi aure, kinga kayan nan ma na jikin ki da zakiji mgn ta danace ki daina sawa idan kuma zaki saka toh ki daura hijjab akai.


  turo baki tayi sannan tace waikai badama nayi ma kwalliya saika gwale ni.

   murmushi yayi sannan yace bahaka bane zahara nagani kuma ya burgeni.


   cikin muryan kuka tace toh ai baka kallaba.


  ahakali ya mika hannun shi ya rike nata duk 2 yana kallon su ,zuwa cen yayi ajiyar zuciya cikin muryar rada yace zahara. dagowa tayi da sauri ta kalleshi cikin ido. yace hannunki laushi.


  da sauri ta kwace hannunta tana rufe ido.


ahankali ya sake cewa zahara zaki iya gane mutumin da ya keta miki mutuncinki?

   gabanta ne ya fadi dan bata taba zatan salis yasan wannan mgn ba .


   muryar haydar sukkaji daga bayan su yana fadin toh iidan kasan shi me zaka mai?


   cikin sauri sukka kalli gurin haydar ne tsaye  hannun shi cikin aljjihun shi.


   salis ya bude baki zayi mgn aka turo kofar falon ,wata budurwa ce agaba bayanta kuma wata matace dagani mahaifiyar yariyar ce


  suna hada ido da haydar ya zaro ido yace me kika zo yi agidan mu?


    babu ko alamar tsoro atattare da ita tace niba gurinka nazo ba, nazo ne ingayawa iyayen ka ina dauke da cikin ka



  

🕊🕊

Mmn Yazeed

            🕊🕊🕊

[8:37PM, 3/25/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*




27 -29




Da sauri ya farajan yariyar yana kokarin barin gidan da ita ummi ce taji hayaniya yayi yawa da sauri ta fito, ganin haydar najan yariyar ta fara dakamai tsawa cikin sauri ya saki yariyar yana mazurai, ummi takalli dadtijuwar matar da suke tare da yariyar tace sannu da zuwa hajiya shigo ki zauna.


  ba musu tahau kujjera ta zauna fatima da salis ko kallo sukabi yariyar dashi.


  haydar ko yana jingine jikin bango sai aikawa yariyar harara take


 ummi ce taji shirun yayi yawa tace baiyawar Allah ban fah ganeki ba.


  kamar jira matar take tace dama ai bazaki gane ni ba amman ai d'aki haydar bazai ce be gane mu ba,  atakai ce dai hajiya Nazo ne na shaida miki 'yata zinat ta dauke da cikin danku haydar



wani zufa me dumi ya karyo ma ummi take ta Fara fadin innalillahi wa Inna ilaihir raju,un maimaitawa taitayi zuwa cen ta daga jajayen idonta ta kalli haydar kanshi akasa yace ummi nifa karya suke min.


 bata ce komaiba ta mayar da kanta kasa wasu hawaye ne masu dumi suka zubu mata zuwa cen ta miki ta nufi falon alhj salis ne yabi bayan ta yana fadin ummi karki gayamai Dan Allah .


 waigowa tayi tace salis wannan ba abun da za,abuye bane , dole ne yasan halin da haydar yake ciki dan ni yanzon ban san yadda zanyi da wad'an nan mutane ba, tana fadin haka ta shige dakin.


   bata dade ba saiga su sunfito tare da daddy yana huce.


   fatima naganin fitowan daddy tamike ta nufi dakin su cike da tsananin tsanar haydar azuciyar ta.


    daddy ko kallon haydar yayi cike da bacin rai sannan ya juya ya kalli bakin nasu  sannan yace kai haydar fita kabar min gida, ku kuma kutashi ku bishi karku kara gigin nufumin gida da nufin Ku kawo min shege bazan taba karba ba.


   haydar ne ya bude baki yace daddy nifa karya suke min.


idan kasakemin Wata mgn zan illataka ka fita kabar min gida wai gawa yayi barayin matar cikin tsawa yace kutashi ku bishi, cikin rawar jiki suka mike suka fita dan tuni haydar ya fita salis ma mikewa yayi zaibi bayan su 

 daddy yace karka fita tsayawa yayi ya jingina kanshi ajikin bango.


 ummi ko kuka take yi tana fadin alhj wannan hukunci beyi ba, matar tabani tausayi be kamata amata hakaba ,yanzon yaya zatayi kenan?


  Oho nidai bazan karbi shegeba d'an karamin shi dashi ya lalata rayuwuwar shi, yace na mashi aure ne ban mashi ba? wacce irin jaraba ce wannan yariyar nan ma ai inbanda jaraba ta girmeshi haka daddy yayita fada wata mgnr ma besanin sanda ta fito bakin shi.


 ummi ko kuka take sosai yayin DA salis ke tsaye jikin bango


haydar ko yana fita ko waiwaye babu ya nufi motar shi shiga yayi ya zauna daidai lokacin zinat da mamarta suka fito harara ya wurgawa Zinat itama ta mayar da nata hararan motar shi yaja yabar wajen.


 yana fita agidan ya fara kuka hawaye ne yake zubomai kaman karamin yaro yana bakin cikin batawa iyayen shi rai da yakeyi amman ya kasa cen zawa, tsawa yayi bakin hanya yayi kuka sosai sannan ya kama hanyar gidan alhj yusuf.


 alhj yusuf naganin haydar gabanshi ya fadi sakamako idanuwan shi dasuka kunbura tahowa yayi ya kamashi ya zaunar dashi ya fara tambayan shi me ya faru amman ina haydar babu baki domin kuwa ya kasa cewa komai illah hawaye dake bin kuncin shi.


alhj yusuf ne ya lura haydar bazaiyi mgn ba, dan haka ya daga waya ya kira daddy.



  daddy na daukan waya yace au gurin ka ya taho, toh maza ka ko reshi karka sake kabar shi a gidan ka mazinaci ne dan iska .


 takaicine ya kama alhj yusuf yace yanzo yaya dan daka haifa kake kira da wad'an nan mugayan kalamen.


ba d'ana bane ayan zun tunda yace shi d'an iskane na barma duniya kuma kaima karka kuskura ka tareni da mgnr haydar yana fadan haka ya katse wayar.


  alhj yusuf ya sauke wayar ya kalli haydar yaga har yanzon hawaye ne a idon sa kamar anbude fanfu


ya mayar da kanshi kasa zuwa cen ya d'ago ya kalli haydar sannan yace haydar aure za,amaka kuma ba ina neman amincewan ka bane za ayi auren ne ko kana so ko baka so.


   *Kuyi hakuri yau banyi typing da yawa ba insha Allahu gobe zanyi me yawa*


🕊🕊

Mmn Yazeed

            🕊🕊🕊

[9:26PM, 3/27/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*



30 - 32



Bece komai ba har yanzon kuka yake yana mamakin zinat anya kuwa ba karya suka shirya mai ba domin shi rabon daya ganta ya dade kuma ai bakai tsaye yake shigarta ba.


  kwanan haydar 2 agidan alhj yusuf zuwa yanzon ya dan saki jikin shi saidai ya dan rame gashi zama agidan ya isheshi dan alhj yusuf ba mata gareshi ba, dan haka gidan babu dadin zama.


 shima alhj yusuf zaman ya isheshi Dan haka ya fara tunanin dawo da salame saidai be saniba ko haryanzo iyayen nashi nanan akan bakan su.


  washegari yanufi gidan dada sallama yayi ya shiga dada ta tareshi da Fara,a itako salamatu tana ganin shi ta shige daki bayan sun gaisa da dada shiru sukayi nadan wani lokaci sannan alhj yusuf ya fara fadawa dada kudurin sa.


 farin cikine ya rufeta har ta kasa boye murnanta daki ta shiga cikin farin ciki amman saita tarar da salamatu tana kuka.


 tana ganin dada tace dada nifa bazan koma gidan sa ba, shekarana uku da dawowa garin nan betaba lekomuba tunda ya karbi yarshi sau 1 ya barta tazo gidan nan be mason tayi alaka dani sabo da ayanzo bana gaban shi dan haka ni bazan saurareshi ba.


 fada dada ta fara tana fadin wani irin tunani ne wannan da baki gabanshi aida bezo gidan nan da niyar zai maidaki dakin kiba kikasan dalilin shi nayin haka ki tunafah tunda ya rabu dake haryau beyi aure ba dayake ke butulu ce har kk wannan mgnr toh tashi maza kije ki saurareshi .


koda alhj yusuf yayiwa salamatu bayani batace a,aba aman fuskar ta adaure take tam kamar bata dariya dan haka hankalin alhj yusuf ya tashi yace salamatu kodai yanzon baki ra,ayi nane?


cikin fushi ta fara zaiyanane mishi kamar yadda ta fadawa dada.


farin ciki ne ya kamashi ashe har yanzon yana nan makale azuciyar ta yana murmushi yace Allah ya huce zuciyar ki nayi kuskure kuma ina neman afuwarki ki yafemin kuma idai fatima ce harsai kin haji da ganin ta haka alhj yusuf yayita rarrashi salamtu harta yadda ta amince sannan ya fada Mata shifa baya son abun ya dau lokaci dan haka suka tsaida akan ranar juma,a me zuwa.


yana barin gidan gidan mahaifin sa ya nufa ya fada masa kudurin sa.


 murnace ta kamasu gaba daya har yadidko godiya sukayiwa Allah tare dayiwa dansu fatan alheri.


   *Ranar juma,a*


taslima da fatima zaune adakin su suna hira taslim tace wlh fatima na kosa atsaida ranar bikin ku.


  tsaki fatima tayi sannan tace


  nidai gaskiya ban kosa ba keni idan ma naji anyi maganar bikin gabana fadowa yake shima yaya kullu maganar shikenan wai ya kosa ranan nan fah har cewa yayi zai gayawa daddy, waishi hakurin shi ya fara karewa



tintserewa tayi da dariya sannan tace ai yadai fad'amiki ne amman ba iyawa zayiba , da dai yaya haydar ne, sake kallonta tayi sannan tace yauwa sister naga wani abu acikin akwatin ki acikin wani d'an karamin akwati.


 "murmushi fatima tayi sannan tace eh yaya ne ya bani"


" taslim ta sake cewa menene aciki?


dafata fatima tayi sannan tace kai taslim kin cika gulma toh nima bansan menene aciki ba kuma yace karna bude sai ranar da akadaura mana aure.


 cafdi ai inda nice wlh saina bude yasan..........


 gud'an da ummi ke rangad'awa ne ya dakatar dasu daga hiran mikewa sukayi atare suka fito suna rige rigen tambayan ummi .


cikin farin ciki ta dafa fatima tace 

 fatima ki godewa Allah yanzon haka mahaifiyar ki tana gidan babanki an mayar da auren su, yazon salis yayi waya yace gashima agidan.


wani farinci ne ya kama fatima ta saki murmushi zuwacen kuma ta fashe da kuka.


ummi ce ta kamota ta rugume tana fadin haba fatima keda zaki godewa Allah kuma, meye na kuka .


  saidare salis ya dawo hannun shi rike da ledoji bayan yayi wa ummi sannu da gida ya kalli taslim yace ke Ina zahara?


 kallon shi tayi sannan tace tana  daki, yaya wai meye acikin ledar?


   "yana tafiya yake fadin inaruwan ki"


washegari


salis ne ya dauki taslim da fatima zai kaisu gidan alhj yusuf murna ce ba kadan ba azuciyar fatima.


 suna shiga gidan suka samu haydar kwace akan kujera yana danna wayar shi salis ne ya nufi gurin shi ya kama kafafuwan shi ya d'aga sannan ya zauna agurin tsaki haydar yaja sannan ya tashi ya zauna salis ne yace wa haydar ina mama?


  atakaice yace tana ciki.

  daidai lokacin  salamatu ta fito daga daki fatima ta tashi da sauri ta nufe ta, tureta tayi ta jawo taslim dake bayanta ta rungume sannan tacewa fatima aike babu ruwana dake.


komawa tayi kusa da salis ta zauna tana turo baki.


 kallonta kawai salis yayi ya sunkuwar dakai.


  mama ko tana rungume da taslim tana tambayan ta karatun ta.


 alhj yusuf ne yayi sallama ya shigo zama yayi cikin su bayan sun gaisa ya tashi ya nufi d'aki


 itama mama mikewa tayi sanna tacewa taslim tashi ki shiga kitchen ki debo muku abinci, tana fad'an haka tashiga d'aki


  haydar ko sai, satan hararar fatima Yake


  salis ko kallon fatima yayi yace ke wai baki iya bada hakuri bane?


 kara turo baki tayi sannan ta kauda Kai, daidai lokacin taslim ta kawo abinci ta ajewa salis nashi sannan tacewa fatima sister zo muci.


  azuciye tace banzanci ba.


" har salis yakai abincin dafda bakinsa yadawo dashi sannan ya kalli fatima yace sabo dame bazakici ba?


saida ta kara turo baki sannan tace toh aini batace dani ba kuma saina kamaci sai kace mayya.


dariyace taso kubucewa haydar amman sai ya dake yaci gaba da danna wayar shi.


  salis ma dakewa yayi sannan yace toh ke wai baki iya bada hakuri bane, kitashi maza tun kafin raina ya baci kije ki bata hakuri.


   mikewa tayi ta fara kuka tana buga kafarta akasa kamar karamar yariya tana fadin nifah ba abinda na mata ni yaushe ma naganta bare na mata wani abu.


  tun salis na kallon fatima har ya gaji ya rufe idonshi dan ya lura yau fatima so take ta rud'ashi.


   shiko haydar baki ya saki yana kallon fatima tuni yanayin shi ya fara cenzawa ji yake kamar ya tashi ya rungume ta


  fatima ce ta lura haydar ita yake kallo dan haka ta tsaya cak tana mamakin shi kuma wannan me yake kallo.


  salis ko yanajin fatima ta daina kuka ya bude ido cikin bacin rai yace meyasa kike min haka ne zahara dan Allah idai baso kk kijamin fushin Allah ba toh ki dakata da irin wannan abun, kije kiyiwa mama sallama kizo mutafi.


   sumi sumi ta wuce ta tura dakin mama tana shiga haydar ya kalli salis yace wlh kai wawane d'an kauye.


 murmushi salis yayi tare da mikewa yana fadin Allah ya shirye ka.


  zuwacen mama da alhj yusuf suka fito fatima na rike hannun babanta .


alhj yusuf yaga salis da taslim tseye yace kardai har zaku wuce?


  salis ne yabashi amsa eh baba zamu tafi.


  yace toh daman Ina son ganinku kaida haydar tsakanin ku wanene akace sun daidaita da fatima?


da sauri haydar ya d'akai ya kalli salis shima salis d'in kallon shi yayi


 🕊🕊

Mmn Yazeed

            🕊🕊🕊

[8:46PM, 3/28/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*



33-37



Alama salis yakewa haydar ya fad'a aman haydar sai make kafad'a yakeyi.


 alhj yusuf yace daku nake mgn fa .


  " taslim ce ta lura salis kunya yakeji dan haka tayi sauri tace baba yaya salis ne.


haidar ne ya d'ago kai ya harari taslim yace ke dan ubanki dake ake mgn


  alhj yusuf yace haydar me yasa bakin ka ya iya furta zagi ne, ai taslim batayi laifi ba abin da tayi kai ya kamata ace kayi amman sai kayi shiru, juyawa yayi ya kalli salis yaga ya dukar dakai yace salis ni dama nasani baban ku ya fad'amin dama naso ne naji daga gareku amman tunda kun kasa magana taslim ta fanshe ku.


   ya juya ya kalli haydar yace toh kai kuma fah.


  baba ni bayanzon zanyi aure ba .


    bata rai baba yayi yace toh sai yaushe?


   idan salis yayi ni daga baya zanyi.


  baka isaba kafison kai ta d'ako mana mgn ai ni inda sosamu ne nan da one week kayi aure dan haka duk abinda akeci nan da Wata 1 kawo yariyar da kk so,Dan mun riga mun yake rana nan da wata biyu dan haka kuje kufara shiri.


haka suka koma gida cike da farin cike sai dai azuciyar salis ranar da akasa yayi mai yawa

 dan haka da suka kebe da fatima yace zahara gaskiya ranar nan da akasa yayi yawa.


 haba yaya wata 2 ne yayi yawa toh ni wlh kusa ma naga yayi min dan nifah wlh tsoron ma ranar nakeji.


 da sauri ya kalleta tsoro kuma toh tsoron me kikeji, kardai ki kecemin tsoron miji kike, toh idai haka ne gara ma tun yanzon ki cire shi dan gaskiya bazaki takurani ba , zahara kinsan fan nayi hakuri


  haharara shi tayi sannan tace hakuri me kayi?


   murmushi yayi sannan yace Zahara Kenan kisan fah kina da kyau kuma na kusa najiki jiki na


kawai daurewa nakeyi karne abin kunya, kasa ya yayi da murya ya Kira sunanta sannan yace kifah shirya dan idan mukayi aure akan kirjin ki Zan rinqa kwana.


 hannuta tasa ta rufe ido dan be saba mata irin wannan maganganun ba.


  murmushi yayi sannan yace zahara idan akace yau andaura mana aure bakaramin farin ciki zanyi ba, bare kuma na ganki ad'akina, Hmmm ranar zan nuna miki irin son da nake miki zan tarairayeki kaman kwai zan nunamiki soyayyar daba kowane namiji bane zai iya nunawa matar sa irin saba.


 kwashewa fatima tayi da dariya sannan tace amman dai yaya sambatu kk KO, wannan irin cin buri ne haka.


  shima dariya yayi sannan yace aidama nasan bazaki gane ba amman ahankali zan ganar dake, mikewa yayi tare da fadin bari naje gurin haydar.


  dasauri tace bayan zon ,muka dawo ba shine har zaka koma, ni wlh natsani haydar d'in nan banason ganin shi.


  shima cikin mama ya kalleta yace zahara kinada hankali kuwa d'an uwan nawa, meya miki ?


 toh yaya ai shima ya tsane ni dan haka nima bana sonshi wlh ko sunan shi aka kira gaba na faduwa yakeyi.


 kallon ta yayi cikin ido yace xahara haydar ba tsanar ki yayi ba haka halinsa yake nima bakiga yana min ba, kuma dan Allah ki yafe masa karki kara kullatan shi aranki kinga d'an uwanki ne , koya miki wani abu kijin haushi toh ki gayamin ni kuma xan faranta miki rai kinji KO ?.

 

 da sauri ta d'aga kai .


  yace kin yafe masa?


  eh tace ahankali.


Shirye shiryen biki nata kankama acikin wannan family ummi shiri take sosai komai ta gama had'awa da  dan ganci na

 fatima dan yazun bikin saura sati 2 kuma har wannan lokacin salis be kawa yariyar da zai aura ba dan haka akabar batunsa dama alhj yusuf ne yaso ahad'a amman daddy tuni yabar zancen haydar kamar yadda yace ya cireshi acikin 'ya'yan shi.


  haydar ne zaune shida abokin sa  anas a harabar gidan su anas sigari kawai yake sha daya shanye wani sai ya kara d'akkowa 


  anas ne ya lura haydar ya kusa shanye kwalin sigarin dauke ragowar yayi sannan yace big boy waikai meke damun ka?


  yana fesar da hayakin dake bakin shi yana fadin fatima.


  Hmm daman aikai ya kamata ka aureta sai da fad'a maka kace bahaka ba sai yanzun da lokaci ya kure zakace wani fatima, kana nufin sonta kk?


 niba sonta nake ba amman ni banason salis ya aure ta, saboda Ina matukar sha,wan yariyar dan haka nafison wani daban ya aure ta, yanzun fah duk tarin 'yan matan dana ke dasu basa birgeni Dana rufe ido fatima nake gani


tsaki anas yayi cikin takaici yace toh yanzon dai saidai kayi hakuri garama ka cireta aranka dan tafi karfin ka.


  tsaki shima yayi yamike yabar wajen tundaga ranar haydar ya zama kamar mara lafiya baya mgn sosai besan me yake damun shiba.


  Yau sauran kwana biyu biki dan haka yan baki sun fara isowa fatima da taslim sai shirye shirye sukeyi  daddy na cikin farin ciki.


  ummi ce ad'aki zaune da kawayenta suna kallon akwati ta zuwa cen saiga salis rike da hannun haydar ummi ce ta kalli haydar tace meya kawoka?

  

 haydar ne yace ummi ninace yazo yaga akwati.


  cikin fad'a tace to tunda kai ka kirashi saika shirya amsan da zakaba babanku idan yadawo ya samu haydar agidan na, mikewa tayi tafita adakin ahankali mutane dake dakin suka fita daya bayan daya.


   haydar ya tsuguna gaban akwati yana dariya yana duba kayan zuwace yace brother kaya sunyi saidai kacika hijjab dayawa aciki.


  murmushi salis yayi sannan yace ra,ayina kenan.


  anagobe daurin aure da daddare salis ya shiga har d'akin su fatima fatima ya hango manne jikin gado ta rufe fuskarta gefe ko kawayen su ne zaune suna hira sunna ganin shigowan shi suka bar daki gaban Fatima yaje ya tsuguna dariya yayi sosai sannan yace zahara duk tsoron auren ne haka, 


  batace kome ba ya sake cewa  zahara dan Allah ki kwantar da hankali bana son ganinki cikin wannan halin .


cikin kuka tace yaya kwata kwata banajin dadi, azuciyata taki natsuwa nayi nayi in natsar da ita nakasa gani nake kamar wani abu zai faru.


  da sauri yace babu wani abu dazai faru zahara sai alheri kiyi tunani dakau kila akwai abinda yake damunki.


   shiru tayi zuwacen tace yaya jiya nayi mafarkin na auri yaya haydar.


  dariya yayi sannan yace ni daman nasan akwai abunda yake damunki dan Allah ki cire tsanar haydar azuciyar ki, kuma kidaina wannan tunanin mafarki ne kawai insha Allahu gobe warhaka burin mu ya cika saida muyi fatan cikawa da imani, haka haydar yayi ta rarrashin fatima harta fara dariya.


  washe gari aka tashi da shirye shiryen dauren aure tun 12:00 bakin daddy suka fara halara kofar gidan ya ciki makil da jama,a sai hada hada ake salis ne ya fito cikin babban riga farare kal yayi matukar kyau waige ya farayi yana neman haydar amman ko alamar shi begani ba dan haka ya shiga neman no barshi tsaki yaje sabo da layin kwata kwata yaki shiga ya koma cikin abokan sa ya tsaya ranshi bace  zucen yaga guri ya kara cika duba agogo yayi yaga karfe 12:43 cikin sauri ya nufi motar shi wani abokin sane yabi bayan sa yana fadin inakuma zaka?


  yana kokarin barin wajen yace tahir yanzon zandawo zanje na dauko haydar ne.


  gidasu anas ya nufa yana tura kofar anas dakin yaga haydar zaune ya tasa sigari cikin zafin zuciya yace haydar kana nufin bazaka halarci daurin aure na bane?


  bece komaiba dan haka yasa hannushi ya fara jawoshi bayan motar ya turashi anas ma ya shiga sun kamo hanya kenan kiran daddy ya shigo wayar salis cikin fada yace kana ina?

  yace daddy ganinan zuwa naje dako haydar n.......


  salatin dasu anas kiyine ya dakatar da shi yana d'ago kanshi yaga Wata babban mota ta nufosu salis yayi kokarin kaucewa amman Ina tuni motar ta fara watan gaririya akan titi.basu kara sani me ya faru ba

zucen haydar ya bude ido ganin shi yayi kwace cikin jini muryan salis yaji yana kiran sunan shi daker yaja kashi ya kalli gurin kwance yaganshi jini na bulbulowa ta cikin shi jan jiki ya fara har ya isa gaban shi ya kama hannun shi babu abun yake kira banda zahara zuwace yayi kalmar shada be kara motsawa ba  haydar ya farajan shi duk da shima ajikace yake.


  karan wata mota yaji yana kallon gurin yaga  daddy da baba yusuf suna tahowa, gurin salis suka nufa daddy ne ya daga hannun shi yace ya innalillahi wa inna ilaihir raju,un Allah ya karbi abun sa😭😭



🕊🕊🕊

[9:04PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*


*Gaisuwa da fatan alheri gare ku*


*Zainab bobbo adamawa*

*Yahancy gombe*  


*bilkisu muhammad*


   *xeeshata*


*mmn abdulnasir*


   *hajju lokoja*


       *Fatyma*


*harda wadan da bankira suna ba inajin dadin yadda kuke nuna sayayyar ku ga wannan lbr*😍😍😘


38 - 39




Tattara su akayi gaba daya aka nufa asibiti har anas.


  nan danan wannan mummunan lbr ya isa kofar gidan daddy dake cike da jama,a yan daurin aure.


  itako ummi daddy ne yamata waya ya gaya mata amman be gayamata rasuwan salis ba yadaice gasu sun wuce asibiti.


hakalinta ne yayi mummunan tashi dan ta dade tana munanen mafarkai akan salis da haydar


  itako fatima tun safe ta kulle kanta ad'aki tana kuka dan haka ummi tace abarta kar agaya mata abari aga abinda allah zaiyi.


  haka gidan ya zama jugun kowa da abin da yake sakawa.


  zuwacen daddy ya sake kiran ummi.


  tana ganin kiran daddy gabanta ya fadi tana dauka tace


  " alhj yaya abin da sauki kodai na taho ne kuna wanne asibiti?


  " cikin jarinta irin na maza yace basai kinzo ba muma gamunan tahowa kuma nasan ke musulma ce kin yadda da kaddara mekyau da marakyau.


kuka ta fara tace alhj kardai kacemin mutuwa sukayi?


  "a,a haydar yanan araye sai dai ya samu karaya acinya"


 kara rushewa tayi da kuka sannan tace salis fah ?


  cikin shashshekan kuka yace sai dai muyi hakuri hafsat salis ya koma ga mahalicin sa.


 ummi jitayi kafafuwan ta bazasu iya daukanta ba take ta yar da wayar ta shiga fadin innalillahi wa inna ilaihir raju,in.


  jin salatin da ummi keyi gaba daya hankalin mutane yadawo gurinta ummi tana kuka tana gaya musu salis ya rasu.


fatima dake kule ad'aki kunnen ta ya fara juyo mata koke koke da sauri ta bude kofar ta fito idon ta jajur bisu tayi da kallo daya bayan daya kowa afalon kuka yake.


  " cikin tsawa tace menene wani abu ne ya faru?


  Wata yayar ummi ce ta jawo ta jikinta nasiha ta shiga yimata sannan ta gaya mata rasuwan salis.


   jitayi kamar an buga mata guduma hawaye kuwa kamar an bude fanfu cikin kuka take fadin nashiga uku na lalace meyasa yayimin haka jiya fah  yace min yau tare zamu kwana shine kuma zai tafi ya barni kai ban yadda ba be mutu ba,nasan shi me cika alkawari ne.


   daidai lokacin daddy ya shigo mutane ne abayan sa dauke da gawar salis d'akin ummi aka shigar dashi da sauri fatima ta kutsa ta cikin mazan ta shige d'akin ,hannu tasa ta bude fukar shi girgizashi tayi tana kuka tana fadin yaya katashi dan Allah.


  daddy na tsaye abayan ta ya kasa cewa komai alhj yusuf ne ya d'agota yace fatima salis yariga ya tafi ki daina mai kuka soyayyar da zaki nunamai yanzun shine kibishi da addu,a


  wani hawaye ne me dumi ya zubo mata alhj yusuf najanta tana waiwayen gawar salis.


   bayan angama gyara salis aka kira ummi tamai addu,a cikin kuka tamai addu,a albarka ko tasamai babu adadi, daddy ne yace akira fatima suyi sallama.


  kamota akayi dan ayanZon bata iya tafiya saitin kunen shi taje babu meji metake cewa.


  daddy ne yoga abin nata bana kare bane dan haka yace afita da ita 


  haka sunaji suna gani aka tafi da salis gidan sa na gaskiya


  fatima ko mawa d'akin su tayi ta fashe da kuka kallon hannuta tayi taga zanen fulawa wani haushine ya kamata tunani yadda zatayi ta goge lallen ta fara 



dan haka ta fara buga hannun ta ajikin bango tuni kyawawan warwaro dake hannun ta suka lanlan kwashi.


  dada ce tahigo taga halin da Fatima take ciki da sauri ta riketa tana fadin meye haka fatima saikace ba musulma ba, dan Allah dan darajan annabi ki dainawa bawan Allah nan kuka.


 suna cikin haka salamatu mahaifiyar fatima ta shigo, fatima ta daga kai tace mama kin ga haydar ya kashe salis KO ?


  cikin tsawa mama tace waye yace miki haka, kifah dai na irin wannan surutun ki kama bakin ki, haydar d'in da kike mgn shima yana cen akwance bemasa inda yake ba.


  cikin kuka tace


  " ai dama bazai san inda yake ba kuma da ikon Allah shima mutuwa zaiyi"


  cikin zafin zuciya mama ta nufi gurin ta gadan gadan



🕊🕊

Mmn Yazeed

            🕊🕊🕊

[9:32PM, 3/30/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*




40 - 41




Dada ce tace haba salamatu ki rabu da yariyar nan, kisan yazon hankalinta ba jikinta yake ba dole abita ahankali.


  fita mama tayi adakin dan bazata iya sauraran irin kalamen dasuke fitowa daga bakin fatima ba.


 bayan sati biyu


fatima ce ita kadai agidan su ummi sun tafi duba jikin haydar dan haka ta wuce dakin su salis  gurin kayan shi ta nufa gasunan jere kamar meshi yana raye tana kamshin turaren shi ke dukan hancin ta dan kaha tasaki kuka meban tausayi da sauri ta juya barayin da takalman sa suke nata kallo tana kuka 


   zuwacen ta farajin muryan ummi tana kiranta tashi tayi da sauri ta fito tana  share hawaye 



   ummi da daddy ta gani tsaye afalo  taslim nagefe tana share hawaye daddy ya kalli fatima yace


   " me yakai ki d'akin su haydar me kike zuwa yi d'akin ?


  kasa tayi dakai sannan tace bakomai tana cikin fad'a ta fashe da kuka.


daddy yace fatima dan Allah ki kwantar da hankalin ki wannan koke koken zai iya jawo miki matsala kiyi hakuri kidaina masa kuka, kuka bashi da amfani agurin mamaci addu,a yafi bukata ayanzon, fatima idan har kin cika masoyiyar shi toh karki sake mai kuka, yanzun nagama ma haydar fad'a tun da ya farfad'o bashi da aiki sai kuka yana kiran salis sai kace ba musulmi ba.


  ummi tace wlh alhj ya kara tayar min da hankali sai mutuwan ta dawo min sabowa.


 " ahankali fatima tace wlh ummi kukan munafunci yakeyi, bayan duk abin da ya faru shi ya jawo"



  gaba dayan su binta sukayi da kallo baki sake, zuwacen ummi tace


  " fatima ashe zargin haydar kk shi yasa tunda ake zuwa dubashi baki taba cewa zaki ba"


  kallon ummi daddy yayi sannan yace kubar wannan maganar, ke Fatima tashi ki wuce d'aki


haka acigaba da tafiya babu wani kwanciyar hankali agidan alhj kasim fatima ta rame tayi baki  duk wanda yasan ta da ya ganta yanzun bazai gane taba.


  duk bayan kwana buyu ummi da taslim suke zuwa doba jikin salis kuma duk randa zasutafi sai suncewa fatima tazo su tafi amman sai tace bazata ba dan haka ummi ta farajin haushin fatima.


  yauma kamar kullum su ummi sun fito cikin shirin tafiya, lokacin fatima na zaune afalo tana karatun Qur,ani taslim tace 


  sister dan Allah yau kizo muje ki gaida yaya haydar jiya fa sai da ya tambaye ki har yana cewa yasan kina cikin damu....


ummice ta d'akawa taslim duka abaya tace wuce muje kada Allah yasa taje ke da yake d'anwan ki ne yazama dole kije amman ita be zaman mata dole ba, sabo da makiyin tane, tana fadan haka suka fita adakin.


  fatima na zaune tun bayan fitansu tana kuka domin kalaman ummi sun bata haushi woto haydar har tambayan ta yake yaji wani hali take cuci saboda yasan yasata cikin tashin hankali afili tace shega dan iska kawai.


 wayarta taji tayi kara ta juya ta kalli wayar no baba ta gani da sauri ta dauka, daga cen cikin wayar baba yace maza ki fito drive ya kawoki asibiti.


  dasaurin ta tace baba kaina ke ciwo bazan ...


  bana son musu fatima koma me yake damunki ki fito kawai .


 tana kuka ta mike tasaka hijjabin ta tayo waje



*kuyi hakuri da wannan*



🕊🕊

  Mmn Yazeed

             🕊🕊🕊

[6:52PM, 3/31/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*



42 -45



Suna tafe  tana kuka har suka Iso asibitin drive ne yayi mata jagora har cikin dakin da haydar yake.


 daurewa kawai tayi ta shiga dan babu inda zata yi.


 mutane ne cike ad'akin wasu ma bata san su ba har kakar su yadidko batace wa  kowa kome ba ta tsaya cen gefe.


  dadace tace Oh ikon Allah KO sallama bazaki mana ba kenan.


 ahankali tace nayi fah.


   yace ke bamu son shashanci wane irin tunani ne wannan ace ke har yanzo bazaki yadda da kandara ba.


 ai lefin ku ne alhj  da bakuci ubanta ba, wawiya kawai mara wayau mama

ce take wannan fad'a


  daddy ya matsa gaban godon da haydar yake yace 


 " haydar ga kanwar ka tazo gaishe ka"


   cikin muryar dake nuna mutun yana jigata yace wacece?


  "fatima ce daddy ya fada atakai ce"


  hannun shi ya fara mikowa yana fadin ina take?


  mama ta jawo fatima ta kaita jikin gadon, d'agowa yayi ya kalli fuskar fatima yace


   fatima kinga salis yatafi ya barmu bamu shirya ba ,a lokacin da muke tsananin bokatar sa.


 idon ta akasa yake amman yana kallon hawayenta na sauka akan hijjabin ta.


 shima cikin kuka ya sake cewa fatima ki daina kuka salis bazai so kukan ki ba, lokacin da abin ya faru sunan ki ne abakin shi gashi ya jigata amman sunan ki radau abakin shi yana fadi zahra zahra sai lokacin da Allah zai karbi numfashi sa sannan ya bari yayi kalmar shahada, idan na tuna wannan abun hakalina na tashi.


  kuka fatima take sosai harda shsheka.


  haydar ma haka zuwa ,cen yace fatima kiyi hakuri ki daina kuka


   daddy yace ya zaka ce ta daina kuka bayan kai gashi kana yi.


  da sauri ya fara share hawaye yana fadin daddy ni ba kuka nakeyi ba.


.  yace toh naji haydar Allah yaye muku abinda yake damun Ku.


  mikewa fatima tayi zata bar waje idanun ta suka sauka akan kafar haydar kubure take tayi suntun kamar zata fashe dauke idon ta tayi domin har yanzun ganin bakin sa take.


  koda suka koma gida ummi batawa fatima mgn ko gaishe ta tayi ayatsune take amsawa.


 haka sukaci gaba da tafiya gidan babu dadi ko kadan har salis yayi arba,in.


 fatima ko ta kara lalacewa.


  daddy ya lura fatima dakin salis take shiga shi yasa hakalinta yaki kwanciyai dan haka yasa aka kwashe komai dake d'akin aka fitar dashi aka rufe dakin


ranar taci kuka kamar ranta zai fita.


  shi ko haydar sai da yayi wata uku cur asibiti amman duk da haka kafar bata takuwa dan haka aka bashi sanda anas ko tuni aka sallame shi.


taslim da fatima ne zaune afalo kowa yayi shiru dan yanzon gidan haka ya koma gani sukayi anfara shigo da kaya ana shiga dashi dakin dake kallon na ummi fatima tacewa taslim wannan kayan fah?


  atakaice tace yaya haydar ne zaidawo dakin yau za,a salamamoshi .


 mikewa fatima tayi zata bar wajen taslim tace sister dan Allah ki rage nuna ma yaya haydar kiyayya abin da kk yi sister yayi yawa gashi har kinsa ummi ta farajin haushi ni ban san me yamiki ba har kk tsane shi haka.


 cikin kuka fatima tace bakisan abin da yamin bafah kk ce ?, duk wannan abun da ya faru waya jawo shi inba shi ba, ai yasan yaya salis bazai so ace baya gurin ba amman ya wuce gantalin shi inda beje neman shi ba da yanzun muna cikin farin ciki, dan haka ni gaskiya bazan taba ganin farin haydar ba, ya cuce ni ya rabani da farin ciki na, ke badan ina tsoron Allah ba dasai na kashe haydar in yaso nima akasheni, dan rayuwana bata da wani amfani



muryan ummi sukaji tana fadin aiko zaki bar gidan nan tun da kin fara fado kalmar kisa bari alhj ya dawo.


 batace komai ba ta koma daki taci gaba da kukan ta zuwa cen taji shigowan su daddy harda babanta azuciyarta tace ankawo Dan iskan nan kenan.


 baya su alhj yusuf sun rako hayadar gida sun koma, ummi da daddy suna zaune abakin gadon da haydar yake ummi tace alhj Ina da magana.


  toh inajinki me ya faru?


  alhj ni gaskiya nagaji da zama da fatima ta koma gurin mahaifiyarta.


 damamaki akan fuskarshi yace me kuma ya faru?


komai ta kwashe ta gayawa alhj haydar najin su .


  nufasawa alhj yayi sannan yace 


   " wlh hafsat kin ban mamaki yazun sabo da Allah fatima zaki biyewa wa , menene ke damun fatima yan zun ban da kuruciya da zafin mutuwan salis dan Allah karki kuma saka wannan mgnr a lissafi idan kinji tana irin wanna mgnr nasiha zakiyi mata ina tabbatar miki da ace nasiha kike mata da tuni ta bari, kuma daga yau inason ki dauki fatima kamar taslim.


 ummi tace shikenan alhj dama ni tsanar da naga tana nunamai ce tayi yawa.


 wannan babu ruwan ki ni nasan maganin abun zama ta bari ne.


  suna cikin haka haydar yace daddy inason na dan watsa ruwa.


  da sauri daddy ya mike ya kama haydar ya mikar dashi tsaye ummi ta mikamai sandar sa daddy na rike da daya hannu shi har suka isa toilet din dake dakin , ummi fitowa tayi ta barshi da daddy zuwa cen shima daddy ya fito.



  washegari da daddare daddy yace wa ummi ki shirya maza kizo  muje  cen babban gida.


 kallon shi tayi tace


    " alhj kana nufin haka zamu tafi mubar haydar shi kadai idan wani uzunrin ya tasan masa fah gashi taslim tana cen gidan.


 gaba daddy yayi yana fadin nifa banason mita kizo muje yan zon zamu dawo.


  haka ummi tabi bayan shi badan ranta yaso ba.


  fatima ko tana ganin fitan su ta sake wani murmushi wanda rabon da tayi irinshi tun kafin rasuwan yaya salis tashi tayi da sauri ta nufi dakin haydar ahankali ta tura kofar ta shiga



🕊🕊

Mmn Yazeed

           🕊🕊🕊

[9:33PM, 4/1/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*



46-48



Ganin shi tayi kwance yana bacci a hankali ta isa gaban shi kare mashi kallo tayi sannan taje saitin kafar dake da ciwon ahankali tasa hannu ta rike kafan.


  ganin da tayi be motsaba yasa ta dage iya karfinta ta murde kafan, kara ya saki me firgitarwa.


uhun da yake besa ta saki kafar ba ci gaba tayi da murdewa.


   haydar ya hada zufa yana kurma ihu zuwa cen ta saki kafar ta matsa nesa da gadon ta kwashe da dariya.


  haydar ko ihu yake yana salati yana kiran ummi da dadddy .


 bayan fatima ta gama dariyarta ta tsaya ta hada fuska sannan tace haydar kadan ka gani indai ni ce kuma da izinin Allah sai an yanke kafar nan, fita tayi adakin ta koma nasu dakin ta kwanta daga dakin tanaji uhun da yake, amman ko ajikin tana cikin bargo ta shige ta rufe idanuwa.


   zuwacen taji shigowan ummi aguje tana fadi ihun me kk yi haydar.


  ganin shi tayi kwance inda ta barshi sai dai ya mirgina yana kokarin kai hannun shi kafar yana fadin zan mutu daddy Ku taimake ni.


  adaran ranar dai basu runtsa ba suna kan haydar kwana yayi yana kuka da kafa dan haka washe gari aka fara cukucukun barin kasar dashi.


 

  fatima ko ranar tayi kwanan farin ciki



da safe alhj yusuf yazo suka dauki haydar aka maidashi asibiti.


bayan tafiyan sune ummi ta shigo dakin su fatima ganin ta tayi zaune tana duba takardun makarantar ta saida ta kare mata kallo sannan tace.


 yanzon sabo da Allah fatima abin kikayi ya dace kenan?


  jitayi gaban ta ya bada dam dan ta zata haydar ya fada abin da tamai ne dan haka ta kasa cewa komai.


 ummi ce ta sake cewa yanzon fatima zakice bakiji ihun da haydar ya kwana nayi ba.


  mikewa tayi mama ni gaskiya banji ba bari naje na duba shi.


 mama tace ai an mayar dashi asibiti inagama kasar za,a bari dan abin yayi tsanani


   washegari aka wuce da haydar       London  domin asake duba lfyr kafan shi.


  *******


bayan tafiyan haydar hankalin fatima ya kwanta dan yazon har tana sakin jiki da kowa na gidan ayi hira ayi dariya amman fah duk ranan da salis ya fado mata haka zata zauna taita kuka har ummi ta saba dan dataga fatima na kuka sai tace abin ya motsa.


  kwanci tashi ba wuya gashi har haydar ya cika wata hudu da tafiya kuma da alamun ansamu na sara dan ayau daddy da baba yusuf zasu dawo dan haka yau ummi taketa garke girke taslim da fatima ke tayata.


 4:13pm su daddy suka iso gida anas ne ya dauko su.


  bayan sunci abinci sun huta ummi ta kalli alhj yusuf tace baku bani lbrn haydar ba.


 yace keda kuke waya kullum kuma kike tambaya na jikin shi, ai nace abin naki ko kara babu ke ki kira salamatu ta kira.


 dariya ummi tayi sannan tace wlh alhj ciwon ne ya bani tsoro dashi nake kwanciya dashi nake tashi  dan gani nake kamar za,a yan ke.


 dariya su alhj sukayi sannan daddy yace ai shima har roko yake wai dan Allah ayan ke mai .


 ummi tace Allah sarki babana ai yaji jiki.


  taslim tace baba yanzon yaya haydar yana tafiya kamar da?


  yace ras yake tafiya taslim ai sati me zuwa zai dawo



fatima ko daure fuska tayi domin kuwa bata ji dadin lbrn ba dan ta tabbatar haydar ba zai bar ta ba dan haka hankalin ta yafi na barawo tashi, sai faman zare ido take.


  ummi tana lura da halin da fatima take ciki zuwa cen tace alhj na gaya muku abin da kuke kokarin shiryawa bazai yiyuba yanzon ka dubi halin da fatima ta shiga.


 hakalin kowa komawa gurin fatima yayi daddy yace fatima me ya faru ?


 dukar dakai tayi sannan tace babu komai.


 alhj yusuf yace dan Allah ku rabu da ita nasan maganin ta  ya nunata da hannu sannan yace wlh karki yadda ki kaini bango dan wlh zanci mutuncin ki fiye da inda bakya zata.


daddy ne yaja alhj yusuf suka fita waje



   bayan sati daya

 ummi da taslim ne keta girkin tarban haydar ummi ta kalli taslim tace taslim fatima tana bani mamaki kiri kiri take nuna tsanar haydar yanzon ki duba fah hatta me gadin gidan nan murna yake haydar zai dawo amman ban da fatima... wayar ummi ce tayi kara cikin rawan jiki ta dauka tana Fara,a tace haydar yaya ka sauka ne?


  daga cen cikin wayar aka bata amsa eh ummi gamu nan ma anas ya dauko ni.


   murna ce ta rufe ummi ta mike ta nufa daki.



   2:58pm suka iso gidan fira suke suna dariya shida anas amman abin da yaba anas mamaki suna shiga gidan haydar ya daure fuska zuwa cen ya fara kwafa anas ya kalleshi yace haydar lfy kuwa ?


  Hmmm anas ina tunanin abin da zanma yariyar nan ne kasan Allah sai tayi nadamar zuwanta duniya



   🕊🕊

Mmn Yazeed

           🕊🕊🕊🕊

[7:55PM, 4/2/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*




49-51




Anas yace wacce yariya kenan?


  " saida yayi kasa da murya sannan yace fatima"


   da mamaki anas yace meta maka, ai kamata yayi yanzon ka rinka tausayawa yariyar nan tun bayan rusuwan salis  saboda ta shaku da salis.


  Hmmm dan ta shaku da salis kuma saita nemi kashini ita fah ta tayar min da ciwan kafar nan saboda taga bana iya tashi tabini har daki ina kwance akan gadona dan tsabar mugunta tazo ta bankaremin kafah.


    ,dariya anas ya fara sai da yayi me isarsa haydar na kallon sa zuwa cen yace toh ya isheka wlh ka kiyayeni ina nan yadda kasanni ba cenzawa nayi ba 



   anas ya gintse dariyar shi sannan yace abin ne yabani dariya kaiko kana kwance kabari karamar yariya kamar fatima ta gana maka azaba, kodai mafarki kayi?


  dariya haydar yayi sannan yace wlh ba mafarki bane toh yazanyi bacci fah nakeyi kawai naji anrikemin kafah ni kasan ma abin da yafi bani haushi idan na tuna uhun da na kurma amman sai naga ta koma gefe tana kyalketa dariya wato zatace tunda salis ya mutu gara nima na bishi.


  anas yace ni kuma atunani na kodai fatima ta gane cewa kaine wadda ka lalata mata rayiwa?


  zaro ido haydar yayi sannan yace bana tunanin haka kaima ka daina wannan tunanin idan ba haka ba zaka sa na fasa abinda nayi niyya.


  da haka suka shiga falon ummi , ummi ko kunya babu ta mike ta rungume haydar shima kwaciya yayi ajikin ta tana buga bayan shi kamar me lallashin yaro yayi bacci tana fadin mu godewa Allah babana Allah ya karbi addu,a mu.


  yana murmushi yace ummi ina godiya da nuna soyayyar ki agareni  bansan kuna sona ba ummi sai da ciwon nan ya kama ni.


 daga kanshi ummi tayi sannan tace haydar akwai wadda zai haifi dansa yace baya so daman cen munason ka halinka ne bama so dan Allah ka gyara halayen ka ka koma kaman salis


 " kasa yayi dakai cikin sanyin jiki yace ummi nima ba ason raina nakeyi ba amman ku tayani da addu,a.


  aidama cen muna maka addu,a amman tunda kace haka zamu daura akan na da, kuta shi kuje kuci abinci, anas ga abinci cen.


    *******


 da daddare daddy da ummi suna zaune afalon daddy fatima tayi sallam ta shigo sanye da hijjab gaban kujeran da daddy yake zaune taje ta zauna ummi ta bita da kallo.


 bayan ta gaida su daddy ya kare mata kallo sannan yace fatima me ya faru akwai wani matsala ne?


   kanta akasa tace daddy Dama inason nakoma gidan yadidko ne.



 murmushi daddy yayi sannan yace kina nufin ki koma cen da zama?


da sauri ta daga kai.


 gyara fuskar shi yayi sannan yace saboda me?



     

  ummi ce tayi karaf tace alhj ka mata ne makiyin ta ya dawo


  da sauri yace kash haba hafsat wai me yasa kk haka wani irin makiyi kuma ita da d'an uwanta ai babu wata kiyayya tsakanin su , fatima haydar d'an uwanki ne baki da wani d'an uwan da ya wuce shi sai kuma taslim dan Allah ku rungumi juna kinga bayawa gareku ba Ku hudu Allah ya bamu kuma ya karbi daya yanzo sauran ku 3 dan haka muke fatan kuhaifa mana yara masu yawa tunda mu Allah be bamu masu yawa ba


 batacewa daddy komai ba tamike tana share hawaye duk suka bita da kallo.


  tana kaiwa kofar haydar na sayo kai ko kallon gurin dasu ummi suke beyi ba ya d'aga hannu ya sharara mata Marika har guda 3


wani wawan tsale ta daka takoma gefe ta fasa wani uban ihu domin kuwa Marin sun shigeta.


  daddy da ummi kuwa mikewa sukayi kowa bakin shi bude suna kallon haydar 


 sai alokacin haydar ya kalli su daddy nan da nan ya fara sosa keya , meta maka, tambayan da daddy yayi wa haydar kenan



ahankali yace bigeni tayi.


 " shine kamata wannan dukan toh Bari kaji daga yau karka kuma kai hannun ka jikinta , in ban da mugunta ma ko kusa dakai bataje ba , mutumin baza kawai.


 ummi ce ta kamo fatima tana  ,duba gurin da haydar ya dake ta fatima ko sai kuka takeyi.


   itama ummi fada ta shigawa haydar yana tsaye kanshi akasa itako fatima tana kwance jikin ummi.


 bayan haydar ya fita ummi takai fatima har daki sannan ta fito ta nufi dakin haydar.


  

 tana turo kofar idonta yayi mata mugun gani haydar ne zaune yana kalon film din batsa ga sigari ahannun shi yana zuka  


  har takai tsakiyan dakin besan ta shigo ba saboda shagala da yayi da kallon salatin da ummi ta rafka ne ya dawo dashi cikin hayyacin shi da sauri ya kashe tv cikin tashin hankali ummi tace haydar  daman abinda kk yi kenan?


  kasa cewa komai yayi jiyake kamar ya nutse cikin kasa.


  ta sake cewa kai dai bazakaji tsoron Allah ba KO?


  nan ma bece komai ba dan haka ummi ta juya ta fita ranta bace.


washegari da yamma alhj yusuf da alhj babbba suka iso gidan su haydar, daman tun kafin sukaraso daddy yasanar musu da zuwan mahaifin shi gidan dan haka ummi ta tanazan musu komai dazasu bukata duk da cewa bata da lfy dan tun sandda tashiga dakin haydar tarasa abun da ke mata dadi.



fatima da taslim KO sunajin tsayowar mota suka rutumo aguje ganin haydar agaban su yasa taslim ta tsaya itako fatima gefen shi tabi aguje taje ta d'ane alhj babba taslim da haydar tare suka iso haydar sai hararar fatima yake.


   alhj babba ko farin ciki ne ya lulubeshi ganin inda jikokin sa suke murnan ganin shi, gaba daya suka rankaya sukai cikin gidan afalon daddy su ka zauna.


  bayan sun natsune alhj babba yace ni banga salamatu ba.


  alhj yusuf yace baba bata jin dadi ne shiya sa bata zoba.


  shiru yayi sannan yace toh Allah ya bata lfy ,juyawa yayi ya kali muta nen dake dakin yace toh duk kubani hankalin ku, wani abun alheri muke shirin kullawa tsakanin haydar da fatima .


  da sauri cikin fatima ya bada kululuuuuluuu yayin da zufa ya fara karyowa haydar.





🕊🕊

Mmn Yazeed

            🕊🕊🕊🕊

[7:55PM, 4/3/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*



52-55



Alhj babba yace in Allah ya yarda nan da sati 2 za,a daura musu aure.


    tuni fatima ta fara kuka, xuwa cen ta koma kusa da daddy ta kama kafar shi tace 


    " daddy dan Allah karka bari ayi haka wlh daddy bana son shi ,ni da ku had'a ni da yaya haydar gara asamu ko almajiri ne ahada ni dashi daddy haydar fah mazunaci ne kuma.... alhj yusuf ne ya daka mata tsawa , hunnun ta tasa dukka biyun ta toshe bakin ta tana fadin na shiga

uku.


  alhj babba yayi tariya irin nasu na manya ,sannan ya kalli haydar yace haydar kai baka ce komai ba.


  kan shi akasa yace  ai alhj da dai zaku cenza shawara da yafi danni inason in aure wayayyiyar yariya ne kuma ma ni ai jinin mu be hadu da wannan fatimar ba.


  daddy ne yace zai hadu nan gaba dan babu wani uzurin ku da zai lalata mana shiri, mun riga mun gama shiryawa.


  haydar babu abin da yake sai share zufah itako fatima kuka take harda majina.


   ummi ko tana gefe ta hada rai maganar fatima ce take mata yawo wai fatima ce ke cewa haydar mazunaci wato ita ta manta da tabon da yake jikinta dan ma ta samu za,a rufah mata asiri  tunanin ummi kenan acikin zuciyar ta.


 alhj babba ya dubi ummi yace hafsat naga kamar bakiyi farin ciki da wannan auren da muke son hadawa bane?


 nan danan ummi ta saki fuska tace alhj ba haka bane akwai dai abin da nake tunani ne kaga yaran nan bashiri suke ba ina jin tsoro abarsu agida su biyu dan  ni dake zaune dasu ni nasan halin su.


 alhj na dariya yace ki daina jin tsora hafsat, babu abin da zai faru dalilin dayasa nace ahada su aure kenan, yusuf ya gayamin halin da suke ci ,dan haka naga idan muka barsu ahaka zasu haifar mana da gadaddiyar gaba, kinga auren da zamu hada su zai dakatar da gabar daman bahaushe yace _*tsuntsu me wayo ta wuya ake kamashi*_


cikin kuka fatima tace alhj indai dan muna gabane za ahadani dashi toh wlh daga yau na bari ,bazan kara gaban dashi ba, dan Allah ajanye maganar auren nan .



 duk falon dariya sukayi ban da ummi da haydar.


bayan alhj ya gama darawa yace fatima ni zakima wayo toh naki wayon aure nan babu fashi idan kinga ba ayiba toh dayan ku baya nunfashi, ya waiga gurin ummi yace hafsat na amshi uzurin ki dan haka acikin gidan nan zasu zauna  kicigaba da lura da irin zaman da sukeyi kafin wani lokaci.


  nan danan ummi ta washe baki tanawa alhj godiya.


  sanna ya sake cewa ke kuma fatima tashi ki hada kayanki kibi baban ki ya kai ki gurin mahaifyar ki kafin ranar daurin auren


 

  sumi sumi ta mike ta fita shima haydar mikewa yayi ya fita


gaba daya kayanta dake gidan ta hada ta fara fitowa dasu ta sawa amotar alhj yusuf har ta gama kuka takeyi motar ta shiga ta zauna har sun fara kokarin fita daga gidan alhj babba ya kalli Fatima yace


 " kinyiwa ummin taku sallama kuwa?


  cikin kuka ta girgiza kai.


 cikin fada baba yusuf yace aiko ranki zai baci.


  da sauri ta fita daga motar har tana tuntube.


 kofar ummi ta tura tare da sallama ganin haydar tayi kwace akan ciyar ummi sai buga bayan shi take kamar me lallashin karamin yaro.


  duk d'agowa sukayi suka bita da kallo har haydar.


 ahankali tace ummi muntafi.


 cikin ya tsuna ummi tace hmmm fatima kenan wai har ke ce kike cewa haydar mazinaci ke kin manta tabon dake jikin ki, ai haydar rufah miki asiri zaiyi kuma kome d'a namiji yayi ado ne .


  har ummi ta gama maganar ta haydar be d'ago ya kalli fatima ba.


 itako fatima kara rushewa tayi da kuka tana me bakin cikin abun da ya same ta gashi har an fara goran ta mata lallai kowaye yaketa mata mutuncin ta ya cuceta take ta tuna sunan da taji abokin sa na kiran sa da shi wato big boy tana tafiya tana fadin big boy ka cuceni in Allah ya yarda sai Allah ya karbamin hakki na dahaka ta isa motar ko ahanya kuka take sosai dan haka alhj babba yita mata nasiha.


  bayan sun sauke alhj suka nufa gida



har suka shiga gida alhj yusuf ko kallon inda fatima take beyi ba, afalo suka samu mama tana kwance akan kujera, tana ganin su ta mike tace alhj lfy na ganka da fatima?


 zama yayi yacire hula sannan ya kwashe komai ya fad'a Mata, sannan ya kara da cewa kiyi mata fad'a sosai dan na kula so suke su kawo mana rabuwan kai , ya kalli fatima yace


  " fatima kece karama Ina rokon ki da ki kwantar da kai kinga haydar ya fiki wayo tunda yayi mgn su daya yaga ba,a goyi bayan shi ba ,be sake cewa komai ba, dan haka kema kiyi hakuri da hukuncin da aka yake akanku , bana son naji  kin sake cewa baki son haydar.


cikin kuka tace toh.


 daga nan be sake cewa komai ba ya tashi ya shiga d'aki.


  mama tasowa tayi ta dawo kusa da fatima ta dafata sanan tace 


   " fatima wai me ya had'aki da haydar ne wannan abin naki yayi yawa fah.


 cikin shashekar kuka tace mama wlh bansan dalili ba nima haka na tsinci kaina.


  shawarwari mama taita bawa fatima har ta dan saki jiki.


ranar da fatima tayi sati 1 dawowa gidan tana kwace afalo hannuwan ta duk suna kan fuskar ta hawaye ne ke tsiyayo mata, tana cikin haka taji sallaman haydar , kara damke idonta tayi kamar me bacci tana jin su suka shigo har takiyan falon shida anas.


  zama sukayi anas na fadin maryan tamu ma bacci take, haydar yaja tsaki yace


    " bawani bacci zama tashi ne"


 daidai lokacin mama ta fito tace a,a su haydar ne?


  eh mama ai mushigo ba kowa afalon sai fatima tana bacci sai ma asace ta bata sani ba


  dariya sukayi har mama amman mama tasan cewa fatima ba bacci takeyi ba.


  komawa d'aki tayi tabarsu afalon .


  mama na barin falon haydar ya mike yaje gaban kujeran da fatima take ya sauke ahannuta ya kama hancinta ya matse.


  da sauri ta fara cikicikin kwacewa tana bige hannu shi.


  sakinta yayi yana fadin munafukkar yariya ai kin kusan shigowa hannu na sai kin gane baki da wayo yar kauye kawai kuma bari kiji na fada miki kin ga wannan hijjaban naki karki sake kizomin dashi gida na ,idan kuma kin ki ji toh kizo dashi ki gani, dashi zan shake ki, ni ba salis bane  ni nan da kika ganni mugu ne 



🕊🕊

Mmn Yazeed

            🕊🕊🕊

[8:17PM, 4/4/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*




56 - 58




Bata ce komai ba in ban da binshi da kallo da take.


 komawa yayi ya zauna sannan ya sakke kallon ta yace 


 meye kika tsare ni da kallo dawani idon ki sai kace na mujiya.


mikewa tayi tana tafiya tana fadin toh me zankalla agurin ka inban da kayan haushi tsaki taja ta shige d'aki.


 haydar ya girgiza kai sannan yacewa anas yariyar nan tana wasa dani, amman ba komai bata sanni bane ba dai zata shigo hannuna ba, saita gane shayi ruwa ne.


  anas ya tabe baki yace kai matsalata dakai baka daukan shawara, matsalar ka yawa gareta



suna cikin haka sukaga fatima ta dawo ranta bace nesa dasu ta zauna tana zubura baki.


  anas ya dube ta yace fatima dama munzo muji ko akwai wani abun da kk bukata sabo da kinga lokaci yana zuwa yama zo.


  kasa cewa komai tayi hawaye na tsiyayowa a idon ta tayi matukar bawa anas tausayi.


   haydar KO yi yayi kamar besan sunayi ba, sai danna waya yake.


   ahankali anas yace fatima kin yi shiru bakice komai ba, kodai na samu taslim ne muyi mgnr?


   kuka ta kara rusawa ta kasa furta komai.


 anas ya mike yaje har kusa da ita yace haba fatima me yasa kikeyin haka irin wannan ai sai kijawa kan ki wani ciyon.


  sai alokacin haydar ya kalleta yace


   " kai kake wani lallabata karabu da ita mana tayi kukanta idonta ne zaiyi zafi, kuma bari kiji na fad'a miki kinga irin wan nan kayan dake jikin ki karki zomin dashi gida na dan ni bana ra,ayin su .


  " ahankali tace ni dama nace ne kayi ra,yin su, ni Ina ruwana dakai"


 mikewa yayi da sauri ya fizgota anas ne ya rike shi yana fadin ya haka ne, kamanta a inda ka ke ne.


 da sauri ya saketa yace ai zan rike ki, kuma karkiga kaman wai ina son ki ne ,ni bason ki nake ba, kuma bazan taba sonki ba amman yazaman miki dole kisamin irin kayan da nake so ,ke dole ne ki kumin biyayya ko kin ki ko kinso.


 mikewa tayi tana tafiya tana fadin wlh baka isa ba wai kai nan har kana ganin kai namiji ne, katon banza dan daudo kawai.


 binta yayi aguje ya ya damke ta ya fara kai mata duka abaki 


fatima ihu take tana kiran mama amman taki fitowa.

.

 daker anas yaja haydar suka fita agidan .


  fatima d'akin mama ta fad'a ta fashe da kuka tace mama kinaji yaya haydar na duka na shine kk barni ya sheni ko?


 muryan mama taji cikin kuka tana cewa


   Fatima me kk son nace muku sai da baban ki yace miki haydar ba sa,an ki bane kece karama ke ya kamata ki kwantar dakai, ya kamata ace yanzon kin hakura kibin umarnin mu kuma da kk cewa na Bari ya kashe ki, idan na ceceki yau idan kk je gidan shi zan biyu ku  ne domin inceceki?



tana kuka take fadi mama toh ai shine yake fadamin bakaken maganganu shi baku ganin lefin shi sai nawa.


 toh shikenan karki bari ke zaki sha wuya ni babu ruwana.


 haka kwanaki sukaita tafiya mama da ummi a nata shirye shirye fatima ko sai ramewa takeyi kulum cikin tunani.


 fatima ce kwace akan sallaya ta kudun dune kanta cikin hijjabi hayaniya muta ne ta faraji afalo ,dumin yau sauran kwana biyu daurin auren.


  cen ta ffara jin gud'a, tsaki taja ta kara kudun dunewa har da toshe kunne.


 tana nan kwace taslim ta shigo da gudu tace sister , da sauri fatima ta mike tace


  taslim sai yau kk ga damar zuwa?


 dafah ta taslim tayi sannan tace fatima meya sameki kk rame haka baki da lfy ne?


  hawaye ne ya fara zubo mata ahankali ta bude baki tace toh ba dole na rame ba, wai arasa wadda za,a had'ani dashi sai haydar dan dai kawai anga babu yaya salis nasan daya nan bazai bari ayi wannan auren ba sabo dashi yasan waye haydar .


  itama taslam kuka ta fara sannan tace


  sister kibar wannan mgnr kema kisan da ace yaya salis nanan baza,ace ki aure yaya haydar ba kuma kema ya kamata kiyi hakuri da yaya haydar din kinga fa kamar su daya banbancin kadan ne.


   cikin fad'a tace wace miki kyaun fuska ko na jiki nake nema, niba kyaun su ke gabana ba nasan naso yaya salis ne saboda kyawawan d'abi,un sa bawai dan wani abu nasaba kamar yadda kk tunani.


  taslim share hawayen fuskarta tayi ta mike sannan tace sister bazaki gane ba, yazon dai ki tashi muje anas najiramu zai kaimu lalle.



itama mikewa tayi tana bin bayan taslim tana fadin ni bazayi lalle ba.


  suna fitowa falon fatima taga mutane cike afalon suna kallon akwati sai d'aga rigunan suke suna dariya daidai lokacin da wata mata tace ikon Allah dube wata riga saboda lalacewa wannan ai da ita gara babu kuma duk su sukafi yawa acikin kayan.


  hjy amina kawar mama tace ai wannan kayan da kika gani Allah kadai gasan kudin da aka kashe gurin sayan su.


  dayar ta sake cewa komai tsadar su ni basu dameni ba dan wlh da ace 'yatace aka kawo wa wannan kayan mayar dasu zanyi haba dubi fah dan Allah sai kace na 'yar arna daga wandona sai wasu yan iskan riguna sake daga wani tayi tace wannan kuma menene?


  gaba daya falon akasa dariya ban da mama dumin matar ta fara bata haushi .


  itako fatima kitchen ta nufa tanajin maganar da matar ke fad'a dan haka ta fara kuka.


  saida mama tasa baki sannan fatima ta yadda tabi taslim, sai dare suka dawo , mama ta kalli fatima tace


 kinga har kinyi kyau, dan Allah kirinkka cin abinci kidan ciko kafin jibi..


 turo baki tayi tare dasa hannuta ta goge fuskarta.


 ana gobe dauri auren ne fatima taita addu,a Allah yasa abin da ya samu salis shima haydar ya faru akansa kafin daurin auren.


  washegari da rana aka daura auren haydar da fatima acen gidan kakan su alhj salisu.


  tunda fatima ta samu lbri an daura auren hankalinta yayi mummunan tashi.


  daddare abokan haydar ne sukazo daukan amarya.


 kuka tayi ba kad'an ba da za,akaita gidan haydar.


  wani sabon gini kayi kafen nasu ummi nan aka nufa da fatima fuskar ta rufe yake.


 abakin gado aka zaunar da ita tana rusa kuka,  bayan kowa ya wuce aka barta ita kai tana kuka ta mike  ta cire gyalen dake jikin ta dauko wani zunbulelen hijjjabin ta, ta saka ,komawa tayi cen lungun gadon akasa ta kwata ta kudundune acikin hijjabin


  zuwacen ta farajin takun ta fiya alamar ana tahowa dakin cen taji an daki kofar garramm.



🕊🕊

Mmn Yazeed

           🕊🕊🕊

[8:15PM, 4/5/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*



*Aslm 'yan uwa da abokan arziki Ina mika gaisuwata agare ku bansan taya zan nuna muku farin ciki naba akan yadda kuke nuna soyayyar ku ga wannan lbrn musam man 'yan group d'ina fadeela lamido novels 👍✔✔✔❤❤*




59 - 60



Kara takurewa tayi guri daya, jikin ta ya hau kerma dan jitayi yau balakin tsoron shi take ji.


  shikuwa haydar ganin bata cikin d'aki ya tsaya yana kallon kofar toilet zuwacen yaje ya tura kofar toilet din ganin da yayi babu kowa yasa shi zagayowa lungun gadon , da saurin sa yasa hannu ya jawota  saida ya jawota har saitin kafarshi sannan ya cikuikuyeta acikin hijjabin , zama yayi bakin gadon sannan ya dauki kafarshi daya ya daura akan cinyarta, saida ya kureta da ido sannnan yace 


  " ina wasa dake ne, bana ce karkizo min da wad'an nan hijjaban ba?


jikinta na rawa tace mantawa nayi.


 yana murmushin mugunta yace eh ai naji dadi da kk manta daga yau idan nabaki umarni bazaki manta ba, mike tsaye.


da sauri ta mike sannan yace ki cire hijjab d'in' ki mikomin


  tana rawar jiki ta cere ta aje agefen shi.


 haydar ya lura fatima ta firgita dashi dan haka yayi murmushi ya kara cewa ki bude kunnuwan ki da kyau daga yau karna kara ganin ki da hijjab, wai ke adole kina boye min breast d'in ki, toh indai nine ko abude kika barsu babu abin da ya dameni dasu idan kuma bakiji ba toh kikara sakamin hijjab kiga ni dake da abin da kk boyewa zaku gane baku da wayo.


 cikin sauri yabar daki fatima taja Wata ajiyar zuciya ta koma bakin gadon ta kwanta ,kasa bacci tayi sai cen wajen asuba bacci ya kwasheta.


washegari


bayan haydar ya gama shiryawa bebi takan fatima ba dakin ummi sa ya nufah.


 yana shiga ta washe baki bayan ya gaidata tace


  " haydar sai yanzon da na ganka hankali na ya kwanta dan d'azon taslim taje kai muku breakfast ta dawo wai tata mugawa ba,a bude ba, sosai hankalina ya tashi dan gaskiya fatima tana bani tsoro.


murmushi haydar yayi sannan yace 



 ummi ki kwatar da hankalin ki bazata yimin komai ba duk cika baki ne kawai.


 shiru tayi zuwa cen tace toh ina fatiman ko bazata gaishe mu bane.


 dukar dakan shi yayi sannan yace 


ummi bacci take har yanzon bata tashi ba .


  tiren dake dauke da kayan kari taslim ta aje gaban shi nan da nan yahau ci suna hira da ummi.


 be dade da faracin abin cinba fatima ta shigo sanye da riga da siket na atamfah tayi matukar kyau .


  ummi ce ta fara ganinta kyau taga fatima ta kara yi mata dan ita kanta rabon da taga fatima babu hijjabi ta manta Kai Allah yayi halitta babu makusa .


  sakin fuska tayi sannan tace


  a,a fatima har kin tashi.


 kanta akasa tace eh ummi ina kwana.


  cikin fara,a ummi ta amsa.


  shiko haydar tun da ummi ta kira sunan fatima ya d'ago kai ya kalleta kasa dauke idonshi yayi har ummi ta lura da haka.


 murmushi ummi keyi sosai tace haydar gyarawa fatima ta zauna kuci abincin tare.


  sai alokacin ya sauke idon shi.


ummi ta sake cewa fatima matsa kuci abincin 


  bata da abin cewa dole ta mike ta isa gurin aksa ta zaune haydar ko yana kan kujera, amman saboda tsabar mugunta yana ganin ta zauna shima ya sakko, hannu ta saka ta fara kai wainar bakin ta ahankali domin tsoron take karta bege haydar.


  takai luma ta biyu bakinta taga ya aje cukalin dayake ci dashi agefe ya saka hannu.


 tana saka hannun ta akan wainar ya daura nashi ya danne mata hannu 'yan yatsun yadinga bi daya bayan daya yana matsewa.


  idon fatima yayi jajur sabo da azaba tun tana daurewa har ta fara mutsu mutsu duk da haka haydar be bari ba dan haka ta saki wata yar Kara.


  ummi ta waigo tace yaya dai fatima?


  da sauri haydar ya saki hannun sannan yace ummi mgn muke.


 tun daga nan fatima bata sake saka hannuta ba har ya gama ci ya mike yayiwa ummi sallama ya fita



yana fita ummi ta dubi fatima tace


  " fatima tashi ki d'ibi wainar kici  naga haydar ya hana ki ci


 damama ki fatima takalli ummi azuciyar ta, tace au dama matar nan tana kallon shi yana gana min azaba mikewa tayi sannan tace





🕊🕊

Mmn Yazeed

           🕊🕊🕊

[4:13PM, 4/7/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*




61 - 63




Nina koshi ta fad'a atakaice.


  kallon ta ummi tayi sosai sannan tace me kk ci dazaki ce kin koshi, tashi maza tun kafin raina ya baci


tashi tayi badan ranta yaso ba guda 2 ta d'iba ta koma kusa da taslim ta zauna.


 bayan fitan ummi ne taslim ta kalli fatima tayi murmushi sannan tace


  " sister wlh yau kin ban mamaki a she dama kina son yaya haydar amman kk cewa kin tsane shi.


fuskar fatima cike da bacin rai tace ni na ce miki inason shi aini tsakani na da yaya haydar babu soyayya har abada.


 tsaki taslim taja sannan tace haba sister ni zaki sa akwana bayan gashi nan har wata kwaliya kk masa na mussaman kuma nagama yau kin aje hijjab a gefe.


   

  toh yazanyi yace baya son hijjabi har fah cewa yayi idan na kara sawa saiya shake ni dashi, 


  dariya taslim tayi sannan tace


 "Allah ya shirye ku"



fatima bata kara tunawa tana da d'aki ba har dare tana barayin su ummi, ci gaba sukayi da harkokin su kamar yadda suka saba.


 kwance take tayi d'aid'ai akan gadon taslim cen ta fara juyo muryan haydar yana fad'a.


 sai alokacin ta tuna da wani haidar da sauri ta karasa bakin kofar, jitayi yana cewa


 " ummi ni gaskiya bazan iya ganin irin wannan kazantan ba a indafah na cire rigata agurin na same shi ba ,abin da ta gyara a d'akin.


 ummi tace nace kayi hakuri, bata kyauta ba, wuce ka tafi gata nan zuwa.


 juyawa yayi da sauri ya fita ummi ko Fatima ta fara kwala ma kira.


 da sauri ta fito gabanta na faduwa, tana isa gaban ummi tace gani ummi.


  saida ummi ta kalleta sosai sannan tace fatima me ya hanaki ki gyarawa haydar d'aki.


ummi ai bece na gyara mai ba, kuma ni mantawa ma nayi da bangaren gaba daya.


 daure fuska tayi sannan tace toh ki wuce ki gyaramai yanzon kuma daga yau karki sake mantawa, dan haydar yaji haushi sosai.


 fatima tana tafiya tana tunanin ummi ita wato bata son ran haydar ya baci, na wani kuma ko oho.


 tana tura kofar falon warin sigari ya daki hancinta.


 da sauri tasa hannunta ta tushe hancinta .


  haydar dake zaune akasa ya mike kafafuwan shi yana busa hayaki ya bita da kallo.


 tana gafda zata shiga d'akin ta yace ke.


 da sauri taja ta tsaya.


 yana mikewa yana fadin me kk toshewa hanci.


bata ce komai ba har ya iso gaban ta, fesa mata hayakin ya fara yana fadin wannan kike toshewa hanci .


  kara matse hancin tayi tace nifah banason warin ta ne 


murmushi yayi me fitar da sauti sannan ya had'aata da bango ya cire hannun data toshi hancin ya matse da daya hannun shi sannan ya fara fesa mata hayakin.



 nan da nan fatima ta rikice tari ta shiga yi babu kaukautawa


ganin da yayi tana neman shidewa yasa ya saketa da sauri.


 tsugunawa tayi tana rige da ciki zuwa cen ta fara  amai.


  haydar na tsaye yana kallon ta, tun tana aman abin da taci har ya koma wani koren ruwa ne yake fita 


  bece mata komai ba har tayi ta gama zuwa cen taja jikinta gefen aman ta kwan ta.


 binta da kallo haydar yayi sannan ya kashe gutun sigarin dake hannun shi ,yayi jifah dashi , gaban fatima yajje ya tsuguna yace ke tashi kije kije kiyi wan ka.


  ko motsi fatima bata yi ba dan haka haydar yaja tsaki, azuciyar shi yace kodai na kira ummi ne, da sauri  ya girgiza Kai , agogon dake daure ahannun shi  ya fara kwance wa sanan yacire rigar dake jikin shi



daukan fatima yayi cek ya nufi dakin sa da ita.


 fatima najinshi babu damar tayi mai musu dan aman da tayi ya galabaitar da ita, jira take taji ya ajeta akan gado domin kwanciya tafi bukata ayanzun , amman sai taga ya nufe toilet da ita.



  kuka ta saka tana kokarin zamewa, kara matseta haydar yayi a jikin  shi sannan ya turo kofar toilet din


  zuwa cen sai gasu sun fito haydar rike da fatima ga dukkan alamu haydar ne ya mata wanka, dan  na hango tsananin tashin hankali atattare da shi.


  fatima ko ban da kuka babu abin da take dan haka suna fitowa haydar ya sake ta sannan yace


  duba fatima kiyi hakuri ki dai na kuka bazan kara taba ki ba, yauma lalura ce, bari naje d'akin ki na dauko miki wata riga ki sanya.


  haydar na fita fatima ta haye gadon haydar lokacin da ya dawo ya sameta ta rufa da bargo bece kome ba ya aje rigar ya fita ad'akin.


 koda haydar ya koma falo kasa zama yayi surar fatima ke masa yayo, wata matsanan ciyar sha,awa ce ta tasarmai wadda rabon dayaji irinta tunkafin rasuwar salis ji yayi bazai iya hakuri ba , gashi bazai iya tunkaran fatima da bukatar saba dan haka ya dauke key din motar sa ya fita


sai da safe haydar ya dawo wanka kawai yayi sannan ya leka d'akin fatima kwance ya sameta akan gado saida ya daure fuska sannan yace


" yaushe kika dawo nan, nace ne ki fito?


 a hankali tace mezanyi toh acen d'in, ni nafi son na zauna ad'aki na.


  gashin ta ya kama ya rike sannan yace 

tashi ki koma idan kuma ba haka ba wlh yazon idan kk fara amai sai kin amaye hanjin ki, kuma ni ba taikonki zanyi ba.


  kafin ya gama mgnr ta sauka da sauri tana fadin zanje dan Allah karka kunna.


 tana fita ya kwashe da dariya tashi yayi yabi bayanta, sai da yaga ta hau gadon shi tukuna ya juya yabar dakin.



barayin su ummi ya nufah yana shiga ya washe baki.


ummi ma murmushi tayi sannan tace ya dai haydar.


yana murmushi yace ummi yau ina cikin farin ciki.


d'aura fuska tayi? tace haydar niko yau akwai abin da ke damuna.


 shima hadiye murmushin shi yayi sannan yace meye shi ummi?


   sai da tayi kasa da murya sanan tace


   " haydar kwana biyun nan ina yawan tuna wannan yariyar da sukazo da maman ta, ko kana da lbrn su ? nasan zuwa yanZon ta haihu KO ?


kanshi akasa yace ummi nifa tun daga ranan ban Kara ganin ta ba kuma ko lokacin da suka zo gidan nan Mufi wata 5 bamu had'u ba dan haka ummi ki kwantar da hankalin ki.


  shiru ummi tayi zuwa cen tace.


 " haydar bakin mgr ka nayi ba amman inason ka kaini gidan su yariyar zanyi mgn da ita.


  kanshi akasa yace shike nan ummi duk ranan da kk shirya sai kiyimin mgn


  shiru sukayi gaba dayan su zuwa ce ummi tace ina fatima yau ban ganta ba


 da sauri ya d'ago yace tanan akwance bata jin dadi.


da mamaki aka fuskarta tace meke damunta?


sun kuyar dakai yayi sannan yace ummi itama kanta batasan kinda yake mata ciwo ba tace nan tace cen, gaba daya ta hanani bacci kuma gashi ta cika shagwaba yan zon ma fah ummi daker ta barni na fito.


 farin ciki ne ya kama ummi cikin sauri ta mike tana fadin bari naje na gano ta , shima haydar bayanta yabi



🕊🕊

Mmn Yazeed

            🕊🕊🕊

[10:03PM, 4/14/2017] Fadila Lamido: 🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*




64 -66




Ummi na gaba haydar na binta abaya,


   dakin fatima ta nufah, haydar ne ya fara sosa keya yana fidin ummi tana daki na fah.


  da saurinta ta juyo atare suka shiga dakin , fatima ko tanajin motsi ta kara damke idonta.


 muryan haydar taji yana fadin ummi kin gani ko , ni jiya kwata kwata ta hana ni bacci amman ita gashi tana yi.


 fatima najin ya kira sunan ummi ta duro daga kan gadon.


   da sauri ummi ta riketa tace kiyi ahankali mana ke da baki da lfy.


  fatima ta bude idonta akan ummi sannan tace


  ummi kin ganshi ya hanani fita wai dolle sai na zauna adakin shi ,ka rashe mgnr tayi cikin kuka


  murmushin munta haydar yayi sannan yace 


  ummi waifah nan kunya taji dan kin ganta adakina.


 itama ummi murmushi tayi sannan ta kara rugumo fatima jikin ta tace fatima menene abin kunya ke da d'akin mijin ki aini yau hankali na ya kwanta, Allah ya kara had'a kawonan ku , ko ma kiyi kwanciyar ki.


 kuka fatima ta kara fashewa dashi tana buga kafarta akasa take fadin wlh ummi ni d'akina zan tafi ai ko jiyama bani nazo ba shine ya kawo ni.


 da sauri ummi tace toh ya isa haka ni ban tambaye ki ba.


  haydar na kallon fatima yana fadin ummi ji abin da take yi haka fah taitamin jiya.


  fatima ce ta wurga mai wani kallo cikin ido tace wlh ummi ni karya yake min.


 daure fuska ummi tayi sannan tace toh ya isa haka ke fatima meke damun ki?


  tana share hawaye tace ni wlh karya yakemin lfy ta lau.


 cikin sigar wasa ya harareta sannan yace amman dan tsabar muguta shine kika hanani bacci daga yau ko zaki kwana kina koke koken ki bazan kara kulaki ba.


   ummi juyawa tayi tana fadin kudai kuka sani



ummi na fita fatima ta fashe da kuka.


 haydar ko daure fuska yayi sannan yace ke fatima kk KO wa, daga yau duk ranan da nayi magana kk sake cewa karya nakeyi zaki gane shayi ruwa ne, tafiya ya farayi sannan yace kuma kafin ki fita ad'akin nan ki tabbatar kin gyara shi , dan ni bana son kazan ta.


 yana fita fatima ta mike tana kuka take gyara dakin bayan ta gama d'akinta ta nufa saida ta gyara ko ina sannan tayi wanka tayi ras da ita.



shiko haydar yana fita bayan gidan ya nufah cikin dan wani lungu ya zauna sigari ya ciro aljihun shi ya kunna ya fara sha, besan meye dalili ba haka nan yaji baya son ya batawa fatima rai dan haka besha ad'akin ba ,sai da yasha ya koshi sannan ya nufa dakin ummi.



 yana turo kofar fatima na sawo kai zata fita ad'akin , da saurin ta kalle shi tatoshe hancita ta kwasa da gudu tayi bayan ummi, tsugunawa tayi ta kudundune abayan ummi.



  da sauri ummi ta mike ta rike ta daidai lokacin haydar ya karaso wajen.,


  KO me ya tuna kuma sai ya fita da sauri.


 fatima na ganin fitan shi ta mike . ummi ta kalleta sosai sannan tace anya kuwa fatima ba aljanu gareki ba, ya za,ayi daga ganin mijinki ki daka wannan uban tsalle.


 wasa da yatson hannun ta take ga kuma hawaye na fitowa afuskarta ahankanli tace ummi nifah banason warin sigari, kuma yaya haydar sai ya dinga sha yana shakamin hayakin.


  da sauri ummi ta dafa kirjin duk da cewa bataji mamaki ba domin kwanakin baya tasan har giya haydar na sha 

saidai tana ganin kamar mutuwan salis yasa 

ya bari , da sauri ta dago kai tace fatima haydar d'in ne yake shaka miki hayaki kina nufin har acikin gidan nan yana shan taba?


  da saurinta ta daga mata kai.


 tace toh shenan zanyi manin abin.



  haka kwanaki sukaita tafiya har aka kwashe wata uku babu wani jituwa tsakanin haydar da fatima , saidai wani abu da fatima bata saniba tun ranan da ya labe yasha sigari yadawo gida yaga fatima na toshe hanci be sake sha ba

dan haka yayi kyau ya Kara haske.



  kaman kullum yau haydar na zaune a office d'inshi anas ya shigo tare da sallama.


 mikawa juna hannu sukayi cikin Fara,a , anas na zama yasa hannu a aljihu ya

dauko sigari yana kokarin kunnawa ,cikin sauri haydar yace


" dan Allah akarka kunna min ita anan kaje waje 


kasha abinka  kasan fatima bata son warinta karkajamin na koma gida tana toshe min hanci


 

  dariya sosai anas yayi sannan yace



 " a lallai Fatima ta samu shiga yanzun kana nufin kabar sha kenan tunda bata so, ko shiyasa naga kwana 2 kabar daukan yariyar ka?


Murmushi haydar yayi sannan yace


" bawai na daina sha bane, inason sha hakura kawai nakeyi ban san me yasa ba konayi niyar sha dana tuna fatima saina maida kasan wani abu dayake bani mamaki kofah awaje nasha sigari ina shiga gidan take ganewa har fah wani toshe hanci zakaga tanayi kamar taga kashi.


  dariya anas ya sakeyi yace nikuwa wlh yadda na saba da sigari babu wata soyayya dazata sa na bari.


 mikewa haydar yayi tare da fadin dallah gabara waya fad'a maka sonta nake inma tunanin ka kenan toh gara ka cenza nime zanyi da fatima yariyar da ko kwalliya bata iya ba tsaki yaja yabar wajen.


  yana shiga gida barayin su ya nufah fatima ya gani zaune tayi tagumi hawaye nabin kuncin ta, har ya wuce ta ya dawo ya tsaya agaban ta , hannuwan shi ya zuba cikin aljihu wandon shi sannan yace ke menene?


   

    cikin muryan kuka tace toh ba ummi bace ta hanina zuwa gidan baba, kuma tabar taslim ta tafi.


   murmushi yayi harda sauti sannan yace


  " shine kika zauna kina kuka  zaman kanki kikeyi kin tambaye ni ne ko ummi ce take auren ki , tamin daidai dan wlh da ace nadawo na samu baki nan harcen zan biki naci miki mutunci.


  mikewa tayi cikin kuka ta nufi d'aki.


 shima bayanta yabi tana shiga dakin ta fad'a kan gado tsaye yayi ya bita da kallo wani yanayi yaji ajikin sa wanda ya kasa fassara shi da sauri yasa hannun shi ya d'ago ta yana fadin tashi ki zauna zan kaiki amman da sharadi .


  tona kuka tace eh naji kafada ni koma menene zanyi indai zaka kaini.


 yana d'an dariya yace ai bawani abu me wahala bane kawai inason ne nizan baki kayan da zaki saka.


  da sauri ta fara share hawaye tana fadin wlh zan saka.


  yana murmushi ya fita adakin zuwacen ya dawo da wasu kaya rike ahannun shi mike mata yayi ta bude riga da siket musu d'an karan kyau aciki sai wani d'an karamin gyale.


  daga kayan take tana kare musu kallo zuwacen tace


   " yaya wadannan kayan fah sumin kadan bazasu shigeni ba"



  tafiya ya fara yana fadin babu wani kad'an da zasu miki idan kinason zuwa ki sa saiki sameni amota.



  ba yadda ta iya tanason zuwa dan haka ta saka ta fito bata shiga barayin ummi ba Kai tsaye ta nufi motar haydar tundaga nesa yabita da kallo.



    bayan sun dauki hanya ma satar kallon ta yake dan idan kaga yadda kayan ya amsheta sai ka rantse da Allah ta saba sakawa, sunyi nisa da tafiya mutar ta tsaya sakowa haydar yayi ya fara yan tabe tabe har ya gaji motar bata tashi ba, dan

 haka yace da fatima ta sakko su karasa da kafah.


koda fatima ta sakkko sai da ta jajjawo rigara sannnan suka fara tafiya


  yamma ce dan haka unguwar cike take da gungu gungu na maxa kuma abin da haydar ya lura dashi duk inda sukabi fatima akebi da kallo take yaji wani haushi ya kamashi, duk da cewa wannan bashine karon farko da ya fara yawo da mace ahakaba, toh meyasa naji haushin wannan tambayan da haydar yayiwa kansa Keenan


wani majalisar samari ya sake hangowa agaban shi gani yayi tun kafin sukai gurin samarin suna waigowa dan haka ya juya ya kalli Fatima ya daure fuska sannan yace


   " ke kina nufin tacikin mazan nan zakibi kuma a haka


  turo baki tayi sannan tace to bakai bane kace na fito haka.


  cikin sanyin murya yace bar wannan maganan fatima kinga ga wani gida nan kishiga ciki kice dan Allah su aramiki hijjab




Mmn Yazeed

[8:52PM, 4/15/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*




67 - 69





Kallon shi tayi sosai sannan ta turo baki tace



    " ni dai gsky baza ni ba haka kawai bansa mutanen gidan ba kuma sai naje aron hijjab.


 kara daure fuskar shi yayi sannan yace fatima Ina wasa dake ne?, maza ki shiga tunkan raina ya baci.



    buga kafa ta fara tana fadin ni dai kazo kawai mutafi nina gaji da tsayuwa.


haydar sakin baki yayi yana kallon fatima  komai dake jikinta rawa yake, hankalin shi kara tashiyayi dan haka ya matsa daf da ita cikin tsawa yace



   " baki da hankali ne bakyaganin mutane na kallon ki?


  "tace toh kazo mutafi mana"


 cikin tsananin bacin rai yace bazamu ba idai har baki shiga kin ara hijjab ba toh sai dai mukoma gida.


 tuni fatima ta fara ganu haydar kishin ta yake , dan haka ta kara dakewa tace



    " aiko sai dai mukoma dan wlh bazanje aro ba, toh wai kai meya da meka dani dazaka ce saina saka hijjab.



  da saurin sa yace bansani ba mara kunya kawai ai zan kamaki ne .


  murmushi fatima tayi tana kallon haydar ta gefen idon ta sai wani hura hanci yake idon shi ko jawur  waya taga ya dauko daga aljihun shi ya fara dannawa matsawa yayi cen gefe dan haka bata san dawa yayi waya ba, tsaye sukayi gaba dayan su, zuwacen ta hango motar anas na tahowa, gaban su ya tsaya da sauri haydar ya bude gaban motar ya shiga.


  anas ne yaga fatima bata da niyar shiga dan haka yace madam shigo mana.


  ahankali ta fara tafiya kamar wadda kwai ya fashewa aciki tana shiga anas yaja motar.



  haydar yana zaune ne ya had'a fuska becewa anas komai ba, ahankali anas ya kalleshi yace



   big boy ya dai ?


take gaban fatima? ya bada damm dan bazata taba manta wannan sunan ba, kuma tun bayan mutumin da ya keta mata haddi bata sakejin ankira wani da irin sunan ba sai yau,



  muryar haydar taji yana fadin wannan fitsarariyar yariyar ce ta batamin rai.


murmushi kawai anas yayi adai dai lokacin suka isa gidan .


 fatima bata saurare suba ta bude motar tafita ko waiwaye babu .


  da murnanta ta shiga d'akin mama dan tunda akayi bikisu bata taba zuwa ba.


 mama na kallon fatima tayi salati sannan tace yau kuma mezan gani fatima abin da bakiyi kina budurwa bane sai yanzon zaki tsiro dashi , duba jikin ki fah duk awaje.


 suna cikin haka haydar ya shigo daga ganin shi kasan yana cikin damuwa dan kuzarin shi ya ragu.


har kasa ya tsuguna ya gaida mama, cikin sakin fuska ta amsa.

.

  kallon shi mama tayi sosai sannan tace.



   Aliyu yau kuwa lfy kake?


  kanshi akasa yace kaina ke min ciwo.



mama tace toh kuma ban da abin ku kai na ciwo bazaku zauna agida ba sai ku kamo hanya sai kace dole, juyawa tayi ta kalli fatima tace 


 maza tashi ku koma gida mun gode da gai suwan.


  kuka fatima ta fara matso wa tana fadin wlh mama lfyr sa lau yanzo.......  mamace ta dakatar da fatima da fadin kinga fah banason mgnr banza ki tashi maza ku wuce gida


  atare suka mike da haydar fuskar shi ayamutse har ya fara tafiya yaja ya tsaya fatima ko tuni tayi waje.


  da mamaki mama ke kallon shi zuwacen tace haydar kanaso wani abune?


ahankali yace mama daman cewa zanyi idan akwai wani hijjab abawa fatima ta saka.


   shiru mama tayi nad'an wani lokaci sannan tace toh bari na dauko mata.


   mama na shiga d'aki haydar ya fita amota ya samo fatima dan anas barin musu motar yayi .


  bayan ya zauna ya kalli fatima yace kije mama na kiran ki.


 cikin haushi ta bude motar ta fita har d'akin mama ta shi tace mama gani.


  wasu zafafan mari taji saukan su har guda uku akan fuskarta, sabo da azaba saida takai kasa.


tuni idanuwan ta suka rine sukayi jawu hijjab taga mama ta wirgu mata akan cinyar ta dauri ta kalli mama.


  hararan ta mama tayi sannan tace maza ki dau ki hijjabin kisan ya idan ba haka ba ko saina jimi ki ciwo wawiya mara wayo yaro dan karami dashi kina neman kisamai hawanjini

ni bansan yadda akayi kika cenza hali daga mutuniyar kirki kika koma ta banza ba


kara matso wa mama ta fara dan haka fatima ta mike da gudu ta saka hijjabin tayi waje.


 bayan motar ta shiga ta zauna haydar na jiyo sautin kukan ta, bece mata kome ba dan ya zaci saka hijjabin takewa kuka.


itako fatima wani irin haushin haydar ne damfare azuciyar dan haka taitama zuciyar ta alkawari itama saita kullamai sharri da har ya mutu bazai manta ba.




*kuyi hakuri da wannan*😘


  🕊🕊

  Mmn yazeed

            🕊🕊🕊

      07014197556

[7:33PM, 4/17/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*





*Godiya Ta Mussamman ga wad'annan group's*



   *Fadeela Lamido novels*👈🏻

*Faty Afreen's novel*👈🏻

*Billy Galadanci's novel*👈🏻

*Firstclass woman's*👈🏻

*Matan Muminai*👈🏻

 *Zee & Hussy novel's*👈🏻

*Big Girl Hausa*

*novels*👈🏻

*HAMA🀠GEE'S NOVEL CHAMBER*👈🏻

*Aisha Hanwa novels*👈🏻

*MF &J Hausa novels*👈🏻

❤❤❤



70 - 72



Har suka isa gida babu wanda yacewa kowa komai tun haydar najin kukan fatima har ya dai naji.


  

bude motar tayi ta fita fuuuu haydar ya bita da kallo cike da damowa sannan ya shiga tunani a fili yace waini meke damuna ne akan yariyar nan  sau nawa ina yayo da mata wayayyu wad'an da had'uwar su ta zarce ta fatima kuma da shigar da tafi wannan lalacewa dan an kallemu baya damu na, amman me yasa na fatima ya dame ni haka, tsaki yaja sannan ya juya ya fita agidan



itako fatima tana shiga d'akinta cire hajjab d'in tayi taje gaban mudubi ta tsaya tana kallon fuskar ta wasu hawaye ne suka sake zubu mata masu dumi saka makon ganin fuskarta da tayi yayi suntum idon ta ko guda daya har jini ya kwanta sabo da marin da mama ta mata.


  tsayawa tayi tai shiru zuwa cen kuma kamar an tsunguleta ta fara tafiya tana fadin wlh bazan yadda ba dan yaga ina mai shiru saiya dinga kullami sharri , da yasan yana da kishin ya dauko kayan da kanshi ya bani, bata cenza kaya ba ahaka ta fita tana shiga barin su ummi ta fashe da kuka kai tsaye ta wuce falon daddy, tana shiga ummi ma ta shigo arude tana fadin fatima lfy?


  Shima daddy arude ya mike yace mamana meya sameki waye ya tabaki?


cire hannuwanta tayi akan fuskarta cikin kuka tace yaya haydar ne yamare ni.


da sauri daddy ya taho ya kama fatima arude yace


   " yanzon haydar d'in ne ya miki wannan duka har gurin ya tashi haka, yasha wani abu ne? , dasauri ya sake hannun fatima ya fara neman no haydar, bugu 2 ya dauka cikin fad'a daddy yace kazo yanzon nan inason ganin ka.


 ummi ko tana zaune tayi tagumi agefe fuskar ta daure


  daddy komawa yayi kan kujera ya zauna sannan yacewa fatima mamana yi hakuri kizo ki zauna idan haydar yazo zai rubuta min sakin ki dan bazan laminci auren duka ba, ai nazaci ya gyara halinsa ne shi yasa har na bari aka had'aki dashi .......



  ummi ce ta katse daddy alhj me kk nufi da wannan mgnr ai yazon tsaka ninsu baza,asan waye me gsky ba sai haydar yazo, kuma ma alhj da kk wannan mgnr ai duk abin da namiji yayi adone ita ka manta cewa rufah mata asiri yayi, dan naga kana nunawa kamar fatima ce kadai taka kuma idan gsky ne ai hannun ka baya taba rubewa ka yanke ka yar.



cike da mamaki daddy ke kallon ummi, juyawa yayi gafen fatima hawaye ne ke zubuwa kamar anbude fanfo, bece komai ba ya maida hankalin shi gurin ummi 


yace naji duk abin da kk fad'a Amman inason ki sani ni agurina da haydar da fatima dukka daya ne, inko har kikaga nafison d'aya acikin su toh shine yafi kyautata min, kuma da kk ce idan hannun ka ya rube baka yankewa ka yar, toh saidai idan kace bazaki iya ba amman ni tuni yaushe zan yanke shi nayar dashi har abada, koko dan haydar yana dan da kk hayfa shikenan baza,a fadi lefin shi ba, kuma bari kiji, Zan baki  last warning duk ranar kk kara cewa haydar rufawa fatima asiri yayi abakin auren ki.


  " cikin sauri ummi ta dafah kirjin ta tace alhaji abin har yakai haka ?


  " mikewa yayi tare da fadin ai yama wuce hak . .....



 turo kofar da akayi shine ya dakatar dasu, haydar ne yayi sallama ya shigo jikin shi asanyaye kallon su yayi yaga kowa fuska bace gakuma Fatima agefe tana rusa kuka.


cike da mamaki ya karasa tsakiyan falon , ganin daddy yayi ya fara takowa gare shi be ankara ba yaji saukan wasu zafafan mari har guda 2, ji yayi kamar antsintsika masa jijiyoyin kan shi, muryan daddy yaji yana fadin Marin da kayiwa fatima ne na rama mata, kuma na baka nan da kwana uku  ka kawomin takardan ta, juyawa yayi barayin fatima sanan yace mamana tashi muje na kaiki asibiti



  suna fita ummi ta mike tana share hawaye ta rikewa haydar hannun tace tashi muje.


ba musu ya mike dakinta takaishi sannan tace


   " haydar meta maka ka mareta?


kwanciya yayi akan gadon ummi


 sannan yace ummi wlh ban daketa ba nifah na sauke ta sannan na wuce.


toh ai kuma haydar akwai shedan duka ajikin ta


bece komai ba gyara kwaciyar shi yayi jefi jefi kuma yana share hawaye babu abin da yafi daga mai hankali kamar maganan daddy na karshe.


  ummi ko tana kula haydar kuka yake dan haka tace



    " haydar wai kukan me kakeyi , zafin marin ne koko sakin da akace kamata ne?


bece komai ba yaci gaba da share hawayen sa


 


gajiya ummi tayi da mgn dan haka ta fita ta barshi 



  washegari 10:00am  haydar ne ke zagaye afalon shi sai kaiwa yake yana dawo wa, saka mokon yau fatima a barayin su ummi ta kwana wai daddy yana nufin dgsk yakeyi toh wai ma ita fatima da tace na mareta meye ribar ta, koda yake ai dama yariyar bakar muguwa ce, tunanin da yayi tayi kenan azuciyar shi, shiru yayi zuwacen ya nufi barayin su ummi.


 ummi na zaune afalo haydar ya shigo tare da sallama 


ko kallon inda ummi take be yi ba, kai tsaye ya nufi d'akin taslim.


  ummi ta bishi da kallo azuciyarta tace kar dai haydar ya kamu da son yariyar nan tun jiya na kula baya cikin hankalin shi.


  shi kuwa haydar yana isa bakin kofar turawa yayi ya shiga dai dai lokacin da fatima ke kokarin saka riga dan haka ya sauke jajayen idon sa akan ta.


cikin sauri ta karasa saka rigar sannan ta d' auki d'an kwali tana daurawa tana hararan haydar.


 bakin gadon yaje ya zauna taslim ko tana daga gefe tana duba wasu ta kardu 


 cikin sanyin jiki yasa hannu ya jawo fatima jikin shi, bata ankara ba saijin ta tayi zaune akan ciyar shi, wannan shine karo na farko da ta haujikin haidar dan haka ta firgita sosai tana ciki cikin tashi amman ina yayi mata irin rokon da bazata iya kwatan kanta ba.


 tun taslim na kauda ido har ta gaji ta mike ta nufi kofah


 haydar yace taslim dawo in dan nine kiyi zamanki, yanzon zan fita



komawa tayi tazauna har yanzon fatima kokarin kwace kanta take.


   haydar ya maida hankalin shi gareta yace meyasa baki dawo d'aki ba kk kwana anan?


  ban sani ba.


murmushi yayi sannan ya sake cewa 


   " dame kika dake fuskar ki kk ce ma daddy nina dake ki?


  cikin rashin kunya ta sake cewa ban sani ba.


  nan ma murmushi ya sakeyi sannan yace


  " fatima dan Allah kiyi hakuri kije ki fad'awa daddy gsky kinga jiya yayi fushi dani sosai, duk abin da kk ji ni kiyi min bana son sharri.


   Kan fatima akasa yake dan batasan me yasaba sam bata son had'a ido da haydar kuka ta fara tana fadin wlh idan baka sakini ba saina had'aka da daddy


turo kofar akayi ummi ce tsaye gaba daya dakin suka d'ago suka kalli ummi nan danan fatima ta kara rikecewa tana tura hannun haydar 


  shiko haydar kara rukuta yake yana kokarin mannata akirjin shi.


  ummi ta kallesu ta tabe baki sannan ta juyar da kallonta ga taslim tace ke taslim tashi kibasu guri.


 har ummi da taslima suka fita haydar na ciki ciki da fatima sai da yaga ta fashe da kuka sannan ya saketa.


  kan gadon ta fad'a tayi ruf da ciki tana cigaba da kuka.


   yayin da haydar yayi tsaye yana kallon ta, kasa tafiya yayi, zuciyar shi na saka mishi wasu abubuwa wanda bazai su faruwan su yanzon ba, ahankali ya sake zama abakin gadon yasa hannun shi ya riko kwankwason ta.


  zabura tayi ta mike aguje tuni d'ankwalin ta ya zame gashin ta ya watse agadon bayanta saida ta kai bakin kofa sannan ta tsaya tace


   Allah ya isa, d'an iska kawai.


   da sauri haydar ya zaro ido fatima ni kk zagi?


  eh anzageka d'in, in banda iskanci Ina ruwanka da kwankwaso na.


  Mikewa yayi hannuwan shi na cikin aljihun shi yace dan na taba jikin ki ne kk cemin d'an isaka, toh wlh idan kk bari na rike ki saikin yabawa aya zakin ta.


 saida ta bude kofar d'ankin sannan tace ai Nina ba kanwar lasa bace  sai kace wata wawiya zan tsaya ka rikeni.


 tahuwa ya farayi Dan haka fatima ta kwasa aguje, sai da taje gaban ummi ta tsaya tana haki.


  ko da haydar ya iso gurin be tsaya ba zuwa yayi zai rike fatima.


  muryan ummi yaji tana fadin taslim d'auko min mayafina kizo mubar musu gidan su karaci iskacin su










🕊🕊

Mmn Yazeed

             🕊🕊🕊



07014197556

[3:02PM, 4/19/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*




73 - 75




Da sauri haydar ya Saki fatima ya dawo kusa da ummi ya tsaya yace ummi yi hakuri na bari.


  taslim ta mikawa ummi gyalenta daidai lokacin da ummi ke fadin a,a aini sai nabar muku gidan bazan iya kallon wannan fitsaran ba.



  da saurin sa yace bafah wani abu bane ummi taki tsayawa ne mgn kawai zamuyi.


  daker haydar ya shayo kan ummi ta koma ta zauna.


  fatima ko wucewa tayi sumi sumi ta shige daki.


  idon haydar akanta har ta shige.


 ummi ma shi tabi da kallo sannan ta Kira sunan shi .


 zabura yayi yace na,am ummi.


  ahankali ummi tace banga kana da niya bawa fatima takarda ba kamar yadda daddyn ku ya bukata.


  wata guntuwar murmushi yayi sannan yace 


 kai ummi yanzon daga kan wannan yar karamar maganan sai ace na saketa, haba ummi ai koshi ma daddyn daya fad'a wasa yakeyi.



  waye ya fad'a maka wasa yake Kai bakasan yadda ya dauki abin ba dan yadda yake son fatima ko Ku daya haifah baya sonku haka.


 nan danan fuskar haydar ta sauya ya fara kokarin mikewa ummi ta kalleshi tace ina kuma zaka muna mgn?


  cikin daure fuska yace ummi kaina ne yake min ciwo zanje na kwanta anjima idan daddy ya dawo zan bashi hakuri.



  murmushin takaice ummi tayi sannan tace aidama nagane nufin ka kaje Allah ya baka sa,a tunda ban isa nabaka shawara kaji ba .



tsayawa yayi  yai shiru zuwacen yayi mgn ahankali ummi bahaka bane amman bari naje nadawo sai muyi mgn.


toh kawai ta furta dan haka haydar ya fita da sauri.


 be dawo gidan ba saida daddare guri karfe 9:30 lokacin daya tabbatar daddy yana gida


 barayin su ya shiga yayi wanka ya feshe jikin shi da turare masu kamshi.


tsayawa yayi ya taje gashin dake kanshi sosai , kyau yayi ba kadan ba dumin kuwa Aliyu haydar namiji ne me cikar suffa da kyan kira duk wani abu da ake bukata awajen namiji Aliyu gadan ga kusar yaki ya had'a su, nima kaina tsayawa nayi na kare masa kallo gsky Allah yayi halitta anan gurin , take tunanin *hafsat* ya fado min ta cikin Fadeela Lamido novels group da tace wai haydar bayi da kyan kira, Hmmm wlh badan ina tsoron kar haydar ya hada miki jini da majina ba dana fad'a mishi😜 dan gsky haydar fa akwai zuciya.


 fitowa yayi cikin kasaita amman zuciyar shi cike yake da fargaba ko daddy zai saurare shi?


  sallam yayi abakin falon ya shiga



ummi na ganin shi ta daure fuska kasa yayi da kansa ya nemi guri ya zauna.


 bayan ya gaida daddy be sake cewa kome ba , ummi da daddy hirar su suka ci gaba dayi .



  zuwa cen daddy ya kalli agogo yace


   " kai bazaka tashi kaje ka kwanta bane?


gyara zama yayi ya zauna akan gwuiwan sa yasa hannun shi daya yana sosa keyan sa.


 daddy ya kara daure fuska yace ko akwai wani abu ne?



  cikin sanyin murya yace daddy nazo na baka hakuri ne naga jiya fatima bata dawo d'aki ba, wlh daddy ni ban dake ta ba..... daddy ne ya katseshi ai dama baza kasan ka daketa ba tun da kasha ka koshi katashi maza kabani guri.



 shiru yayi kuma yana nan a inda yake sai yau yasan fatima ta zama wani bangare na jikin sa domin ji yake yau idan daddy be bashi fatima ba , toh yau bazai iya bacci ba.



   hawaye ne suka fara zubo mai daddy ya bishi da kallo take tausayin sa ya kamashi Amman sai ya dake yace wai haydar banace ka fita kabani guri bane.



  Saida ya share hawayen sannan yace daddy wlh zan iya rantsewa da Qur,ani ban dake fatima ba.


  shiru daddy yayi zuwa can yace jeka ka kiramin fatima.


  zuwacen suka shigo yana gaba fatima na baya ummi ko tana zaune ta had'a fuska.


 daddy ne yayi mgn cikin kausasassiyar murya fatima haydar yace wai be dake kiba, yace zaiyi rantsuwa ko kema zaki iya rantsuwa cewa ya mare ki?


 shiru tayi tana wasa da yatsun hannun ta hankalin ta tashe.


 daddy ma kallonta yake yana na zari zuwa cen ya sake cewa mamana yanaji kinyi shiru?


 nan ma bata ce komi ba.


 daddy ya danyi murmushi sannan yace


  ga dukkan alamu mamana bata da gsky.


kuka ta fara duk suka bita da kallo, ahankali daddy yace fatima ki gayamin menene ya faru.


Cikin kuka tace ai shine yaje gurin mama ya kullamin sharri yasata ta dake ni, ta kwashe komai ta fad'a .


dariya daddy yayi sosai San nan yace toh ai baki yi lefi ba kinyi daidai ' san nan yace kai kuma kaSan bakaso me yasa ka bata kayan kace ta saka.


 cikin sauri haydar yace daddy aini bance ma mama kome ba, nidai kawai nace ne abata hijjab.


 fuskar daddy sake yace toh yanzon dai haydar kayi kuskure  Saika kiyaye gaba, ya juya ya kalli ummi yace baki ce kome ba.


 toh Alhj me zance aini yanzon haydar yafi karfi na.


nisawa yayi sannan yace nagama duku kutashi Ku tafi.


fatima ce ta fara mikewa tayi gaba tana kuka.


  tana fita daga barayin su ummi kafin ta karasa nasu taga wata bakar mage, aguje ta juya tana ihu daidai lokacin haydar yafito , ji yayi kawai an cikuikuye shi duk da haka bata natsuba sai kara kwakume shi take.


rungumeta yayi sosai ajikin shi yana fidin fatima menene?


 gani yayi bata da niyar mgn dan haka ya dauketa cek .


 kan gadon shi ya ajeta amman sai taki kwanciya tana dad'a kamashi, tuni yanayin jikin shi ya fara cenzawa shima gadon ya hau ya jawota jikin shi sannan yace fatima menene ya baki tsoro ?


ahankali tace mage ce.


murmushi yayi sannan yace yanzo magen ce tasa kk rude haka?


  bata ce kome ba ta Kara mannewa ajikin shi tana maida ajiyan zuciya.


 ahankali ya fara buga bayanta ji yayi kamar tayi bacci dan haka ya fara shafata.


  zabura tayi ta mike sakamakon hannu haydar da taji akirjin ta.


 saida takai karshen gadon sannan ta tsaya.


 shiru haydar yayi yana maida nunfashi gsky yau banzan iya hakuri ba dan tariga ta motsomin sha,awa ta ,tunanin da yayi kenan azuciyar shi , dan haka ya dauki wani filon shi me laushi ya jefeta dashi.


 ihu ta kurma ta daka wini uban tsalle ta dire jikin haydar tana fadin yaya haydar dan Allah ka rakani gurin ummi



🕊🕊

Mmn Yazeed

          🕊🕊🕊🕊

[7:59PM, 4/20/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*




76 - 78




Kara menneta yayi ajikin shi sannan yace ki kwanta kawai babu abinda zai same ki.


   cikin kuka  tad'an ture shi tace nidai gsky kazo karakani bazan iya kwana anan ba.


 daure fuska yayi sannan yace ke babu inda zani idan zaki kwanta ki kwanta ni karki dame ni.


bata kara cewa komai ba ta lafe ajikin shi, zuwa cen taji ya ci gaba da taba ta , da sauri tasa hannunta tana tura nashi daga jikin ta.


 cikin raunanan niyar muryar yace ki bari mana nifah mijin ki ne.


 a,a bawani miji ni gaskiya ka bari bana so.


  ahankali ya sake fadin nima ai ba cewa nayi kina so ba nine nake son hakkina.


   tashi tayi tsam daga jikin shi tana kokarin sauka agadon.


  da sauri ya jawota yace wlh idan baki daina ba zan fita na rufeki ad'akin nan bagen ta kashe ki.


 cikin sauri ta tura kanta cikin kirjin shi tana fadin nabari


  ai daga nan haydar ya samu abin da yake so domin kuwa kwanciya tayi kamar me bacci haka haydar yayita wasa da ita, jin da fatima tayi yana neman ya wuce iyaka yasa ta fara kuka domin har ya fara raba ta da kayan jikin 


  koda yaji tana kuka be saurara mata ba illah ma karfi daya fara gwada mata dan yaga kokarin guduwa take.


  Nidai danaga haydar da gaske yakeyi tashi nayi suf suf nabar musu d'akin.


 ina daga bakin kofah, zuwacen na fara jiyo ihun fatima tana kuka meban tausayi tana ma haydar magiya kayi hakuri dan Allah dan darajan annabi ka kyaleni, waiyo Allah na nashiga uku , haka fatin taita kuka  saida aka kira sallahn subahi sannan haydar yabar fatima, idan me karatu be manta ba haydar dama ta wannan fannin ba daga nan ba.


 ********


 wanka ya fito ya tsaya yana karewa fatima kallo kai gaskiya yau ya kwashi garan da be taba jin irin shiba Ashe duk tarin yan matan da yake dashi duk shirme ne, fatima da yake rainawa yake ganinta kamar wata yar kauye ta fisu gard'i kallonta yayi yaga ta kwanta kamar gawa azuciyar shi yace Allah sarki Fatima anya kuwa zaki iya daukan d'awai niya ta, da wannan tunanin ya wuce masallaci, 



  yana fita fatima ta bude idon ta ahankali hawaye ne ya biyo baya, ahankali ta zame ta sauka akan gadon, da rarrafe ta shiga toilet.


 zuwacen ta fito tana bin bango ahankali ta tsuna ta dauki duguwar rigarta dake yashe akasa ta maida jikinta domin babu kayanta ko guda daya adakin haydar , taso ta fita adakin ta koma nata amman bazata iya ba dan haka ta koma kan gadon ta kwanta.



  bata dade da kwaciya ba haydar ya dawo, kai tsaye ya nufi bakin gadon yana kallonta ya gane tayi wanka amman idonta har yanzon arufe yake.


 saitin kunneta yaje yace zahra shine kk koma kan gadon baki bari na gyara miki ba.


 da sauri ta bude idonta dan ji tayi kaman salis ne ya kira sunan ta tana ganin haydar tamai da idonta ta rufe, ta fashe da kuka.



hannun shi yakai ya taba gushinta yace yi hakuri fatima ki daina kuka.


 itama hannunta takai ta bige nashi taci gaba da kukanta.


  shiru yayi na wasu dakikai yana tunani zuwacen yace



  fatima dan Allah kiyi hakuri ki daina kukan nan zai iya jawo miki wani ciwon, kinji


  batace dashi komai ba haka yayita mgn har ya gaji karfe 8:00 yace fatima zantafi Office kinga lokaci ya kure.


banza tayi dashi har ya fice.


 ummi naganin haydar gabanta ya fadi saboda yadda ta ganshi da ganin shi akwai abin da yake damun shi tace haydar yadai me kake yi har yanzon baka wuce office ba?


 jikin shi asanyaye yace makara nayi yazon zan wuce, Ina taslim ne ?


 da sauri ta fito daga kitchen tana fadin gani.


 ko kallonta beyi ba yace fatima na kiran ki.

 toh kawai tace a takaice.


 koda taslim taje fatima bata daina kuka ba kuma bata ci abinci ba haka ta gaji da tambayan ta meya sameta, amman babu amsa.


ahaka har aka kwashe kwana biyu yadda aka aje abincin fatima haka ake dauka, haydar ko yayi lallashin har ya gaji dan haka abin ya fara bashi tsoro.


ranar da suka cika kwana 3 ahaka da safe haydar yana zaune afalo taslim ta shigo, gaidashi tayi ta nufi dakin fatima.


muryan haydar taji ya kira sunnanta ta dawo ta tsaya ,cikin sanyin murya yace


  taslim wai fatima batacin abinci ne kwata kwata ko akwai wani abun da take sone daban.


 tace yaya wlh nima ba yadda banyi da ita ba, ta fadamin abin da take so na dafa mata, amman ko mgn bata min.


cikin mamaki yace kina nufin kema bata miki mgn?


kaita daga. yasake cewa ummi ta sani?


  eh nagaya mata tace wai babu ruwanta.


Shiru yayi zuwa cen yace shike nan jeki.


tana shiga haydar ya mike gurin ummi ya nufah.


tana zaune afalo tana amsa waya kusa da ita yaje ya zauna ya daura kanshi akafadar ta.


 tana gama wayar ta waigo ta kalleshi tace yadai na fatima meya same fatiman taka kwana 2 ?


 cikin shagwaba yace ummi bayan kinsan halin da muke ciki amman baki kula muba.


 d'an murmushi tayi kad'an tace aini baku sakani aciki ba, sai kanwarka ka kira.


murmushi yayi kadan sannan yace


toh ummi ai ta kasa dole sai kinsa mana baki.


 tace toh inajin ka menene ya faru?


saida yayi kasa dakai sannan yace ummi laifi na mata kuma na lallasheta taki kulani.


da saurinta tace toh yanzon me kk son ayi?


dagowa yayi suka hada ido da ummi sannan yace ummi hakuri zaki bata.


kallon shi tayi sosai sannan tace ikon Allah ashe akwai lokacin da zanga wannan ranar, haydar ashe taurin kanka na banza ne tunda gashi lokaci 1 mace na shirin susutaka, wai yau kaine ke rokon aba fatima hakuri.


  mumurshi yayi sannan yace nimafah bansan yadda akayi na samu kaina ahaka ba, ummi idan fatima na cikin damuwa sainaji duk banajin dadi


 itama tana murmushi tace aini tuni na lura da haka, saidai fani gsky yadda fatima take nuna kiyayyar ka haushi take bani.


da sauri yace ummi ki daina jin haushin ta, in Allah ya yarda Wata rana zata bari.


mikewa ummi tayi tace toh shikenan haydar tunda kaji ka gani tashi muje naga ginbiyar taka.


suna cikin tafiya ummi ta kalli haydar tace haydar bari na baka wata shawara kaga wannan kananan kayan kadaina saka su karinka saka manyan kaya kamar yadda salis keyi, d'aga kanta tayi ta kalli gashin kanshi tace haba haydar ai ko nice fatima bazan soka ba jifa inda ka tara gashi saikace bishiya, wannan gashin naka bazai rasa wari ba.


  da sauri ya tintsere da dariya ya tura mata kan yace haba ummi shinshina kiji kullum fah sainaje an gyaramin shi.


da sauri ta kauda fuskarta tace bazan shinshina ba, kaje ka askeshi kawai.


yana dariya yace toh shikenan ummi zan aske


da haka ummi ta tura d'akin fatima ta shiga haydar nabinta abaya.


  taslim ko na zaune agefen fatima tana danna wayar ta yayin da fatima ke kwance agado tayi ruf da ciki.


  ummi ta kalli taslim tace har yanzon dai zaman kuramen kuke?


 taslim tace toh ummi taki magana.


karasawa bakin gadon ummi tayi ta zauna sannan ta dafah bayan fatima tace fatima


can ciki ciki ta amsa, ummi ta sake cewa tashi ki zauna.


ahankali ta fara kokarin tashi haydar ko nacen gefe kamar munafi hannuwan shi cikin aljihun shi.


 baya ta zauna ummi ta kalleta sosai taga har tadan fad'a tace.


 fatima wai meke damunki ne haka me yayi zafi?


nan danan hawaye ya fara zubo mata zuwacen ta fashe da kuka.


 da sauri ummi ta jawota jikinta ta rugume tana fadin ya isa.


daker ummi ta shawo kan fatima tayi shiru , shiko haydar tunani yake azuciyar shi wannan wacce irin yariya ce.


 ummi ta sake cewa haba 'yata kidaina daukan abu da zafi haka, haydar ya fad'amin shine ya miki laifi , kisan abin da nake so dake daga yau idan ya sake bata miki rai kizo ki gayamin duk hukun daya dace dashi ni zanmai karki kara tada hankalin ki, kinji ?


ahankali ta daga kai.

 

ummi tace yauwa ko kefah yanzon dai mgnr ta wuce ko?


 murya cen ciki tace eh.


toh Sakko kici abinci.

sakkowa tayi ummi da kanta ta zuba mata  .


kwana biyu haydar ya dan samu sauki gurin fatima dan yanzon bata harara shi kuma yanaji tana mgn da muta ne 


 

 fatima ce zaune adakin ummi suna hira ummi tace fatima yaushe zaki fara girki ko kunfi son kuyita cin namu.


    ta bude baki kenan zatayi mgn haydar ya yayi sallama ya shigo.


    tana daga kai ta kalleshi,tsaye yake cikin manyan kaya wad'an da suyi matukar karban shi ta zabura aguje ta nufeshi kamshi  turaran da taji shi ya tabbatar mata dawa cewa ba salis bane dan bada wannan turaren yake amfani ba tsugunawa tayi ta fashe da kuka.


 ummi ma hawaye ne ke zuba a donta, shima kansa haydar d'in fatima ta bashi tausayi 


  juyawa yayi ya koma barayin su cikin tashin hankali yana zama ya fashe da kuka.


   fatima ko bataso haydar ya fita ba ji tayi tana balakin son ta hada ido dashi dan idan ta kalleshi ji take kamar taga salis dan haka cikin sauri ta mike ta nufi dakin su.


 tana shiga ta samu  haydar zaune afalo idon shi jawur.


 zama tayi akujeran dake kallon nasa ta kure shi da ido tana hawaye.


 mikewa yayi yazo gabanta ya tsuguna ya fara share mata hawayen yana fad'in baxan kara saka irin wannan kayan ba fatima, da nasan cewa zaku shiga wannan yanayin har kuna zubar da hawaye ke da ummi da banyi ba, cire hular dake kansa yayi aje agefe.


 da sauri fatima takai hannunta ta dauka ta daura mai akai tana fadin karka daina yaya wad'an nan kayan sunfi maka kyau.


  ya bude baki zaiyi mgn wayar shi tayi kara, ciro wayar yayi a aljihun sa ya duba sannan ya aje agefen fatima, mikewa yayi ya fita da sauri yana fadin Ina zuwa fatima.


  harya kule fatima na kallon shi , yana fita ta juyar da kallon ta gawar da ya bari da sauri ta dauki wayar tana share hawaye, ta shiga dannawa.



 *Toh masu karatu gadai fatima ta dauki wayar haydar KO me zai faru ?*



 

🕊🕊

 Mmn Yazeed

             🕊🕊🕊

[8:59PM, 4/21/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*




79 -80




Tsinta kanta tayi dason kallon hoton dake wayar dan haka ta fara dubawa.


dayawa daga cikin hotonan haydar ne shi da salis wani suna dariya wani kuma kaga sun ware kamar zasuyi danbe, kallo take tana hawaye tana tuna soyayyar da salis ya nuna mata, kai da ace har yanzun salis na nan tohni yar gata ce, da wannan tunanin ta fita daga gurin .


wani gurin ta sake bud'awa innalillahi wa inna ilaihir raju,un shine kallaman daya fara zuwa bakin ta domin kuwa hotunan haydar ne birjik tare da yanmata kala kala cikin shigar lalacewa da nuna tsaraici domin kayan dake jikin su dashi gara babu, kwata kwata babu kyan gani.



  take taji wani haushi ya taso mata wani bacin rai taji wadda rabon da taji irin shi tunda akace za,a had'ata aure da haydar.



  hawaye taji suna zubu mata, da sauri tasa hannunta ta shafo ta kallah, menene wannan ? tabayar da tayiwa zuciyar ta kenan, kardai ace son haydar nake, dakuwa naci amana, naso wa kuma dan bani da hankali sai naso kani.


mike wa tayi ta aje wayar har ta juya sai kuma ta dawo ta sake daukan wayar wani bangaren ta sake shiga hotun haydar ne shida anas zuwacen ta ?fara cin karo da wasu hotuna da suke neman dauke numfashin ta. bakinta bude ido bude duk sun firfito waje take kallon hotun tabas wannan itace lokacin da take amsa sunan daniju, wanda ko ke kanta haydar ne gashi nan danne da ita akan kujerar motar yana kokari yage mata riga take sunan da anas ya kira haydar dashi kwanaki ya fado mata BIG BOY


  take ta kwallara wani kara saida gidan gaba daya ya amsa, jitayi kafafuwan ta bazasu iya daukan ta ba dan haka ta fadi kasa timm.

,

  aguje su ummi suka shigo ita da taslim haydar nabin su abaya.


  a gaban fatima suka tsuguna suna kokarin dagata suna tambayan ta menene.


 shi ko haydar fadi yake ummi yanzon haka mage ta gani kisan matsoraciya ce.


 fatima KO hannu ta daga tana kuka take nuna haydar tana fadin shine wlh haydar ne shine wanda ya cuceni , wlh shine ummi, shine gashi nan agaban ki  Allah ya tonamai asiri.


 haydar sakin baki yayi yana kallon fatima



ummi ko gani take kamar fatima aljanu gareta.


 dan haka tacewa taslim kiramin daddyn ku ya samo mana malami amata rukiya.


  Matsowa haydar yayi yana fadin babu wani aljanu ummi yanzun haka be wace mage ta......... wayar shi daya hango agefen fatima shine ya dakatar dashi da sauri yakai hannun shi ya dauki wayar , zamewa yayi akasa ya zauna sannan ya cire hular dake kansa ya fara fifita yana fadin Inna lillahi wa inna ilaihir raju,un.


 da sauri ummi ta juya gurin haydar tace toh kaikuma meya same ka.


 basu ankara ba sukaga fatima tayi waje aguje, yayin da haydar ke fadin shikenan ummi nashiga uku.


  taslim ce tabi bayan fatima da gudu ummi ko tana gun haydar sai fifita take mai zuwacen ta fara girgiza shi tana fadin haydar wai meke faruwa kar ku maidamu mahaukata mana.


  itako taslim ko da ta fita kofar gidan babu fatima babu alamarta juyawa tayi tana kuka.


 tana shiga tace ummi ban ganta ba.


  da sauri haydar ya daki bango.


 cikin bacin rai ummi tace taslim wuce muje tunda bazai gaya min abin da ke faruwa ba, Allah ya baku sa,a.


  ummi tana komawa barayin su ta kira daddy awaya ta fad'a mishi halin da suke ciki.


    ba,a dade ba  saiga daddy ya shigo d'akin su haydar ya fara shiga, samun shi yayi ya hada kai da gwaiwa.


  kiran sunan shi yayi haydar, da sauri ya dago kai ya kalleshi yace taso muje.


mikewa yayi sumi sumi yabi bayan shi bayan sun shiga motar daddy sun zauna daddy ya kalleshi sosai yace 


 " me ya hadaka da fatima harta wuce gidana ta tafi gidan mahaifin ta?, babanta yayi min waya cewa gata tazo ko mayafi babu kuma tunda taje ta kasa mgn illah fadin haydar ne, haydar ne, me ka mata dahar ta shiga wannan yanayin ?



  kasa mgn yayi ya dukar da kanshi cikin matsanan cin tashin hankali.


daddy yasake yin mgn haydar badakai nake mgn back.


nan ma shiru babu amsa



daddy yace kana nufin bazakayi mgn ba kenan?


  kara dukar da kanshi yayi kasa danji yake kamar kasa ta bude ya shiga.


 kallon shi daddy yayi cikin takaici sannan yace 


  nakula baka da gsky tunda gashi ka kasa mgn , ummi ya kira awaya tana dauka yace dauko gyalen ki kizo muje , basu juma ba ummi ta fito.


 gidan alhj yusuf suka nufah.


 suna shiga cikin falon fatima ta mike da saurinta tace baba gashinan yazo shine macucin dakace idan ka ganshi zaka karban min yanci na , yau gashi agaban ka.


 baba ne ya daka mata tsawa sannan yace koma ki zauna .

batayi musuba ta koma ta zauna sannan ta runtse idonta tace wlh baba bana son ganin haydar arayuwata  tunda na fara sanin kaina yake cuta ta.


ahankali daddy ya matso inda take yace fatima gayamin wanne irin cutar dake haydar keyi?


 kowa afalon ita yake kallo , haydar ne kawai kansa ke kasa.


cikin kuka fatima tace daddy haydar shine mutumin da yayi min fyade tun da kankanin kuruciya ta.


ummi ce ta mike dafe da kirji tace lallai fatima yau na tabbatar baki kaunan haydar ai basai kinmai sharri ba, dan kina son rabuwa dashi , muyar daddy taji yana fadin 


  ke banson mgnr banza keda kk wannan surutun shi haydar din kinga ya musa ne.


  da sauri ummi ta kalli haydar taga ya kasa daga kan shi sai hawayen dake digowa, itama kuka take tace haydar da gaske ne?


  bece komai ba illah kukan sa daya karu har mutanen dake falon na iyajin sheshshekan kukan sa.


 kuka ummi ta fashe dashi tana fadin nashiga uku Allah ka dauki raina na huta daganin wannan abin takaici.


mama ce ta dafah ummi tace bar kuka dan Allah ai tama kona gidan sauki.


 cikin fada daddy yace wanne sauki ai babu wani sauki, Kai haydar maxa katashi kabar wajen nan tun kafin na kwashe maka albarka, kuma aure tsakanin ta dakai babu dan iska me abin kunya kawai ina takaicin ka amatsayin dana tari ya fara babu kaukautawa haydar ya tashi da sauri ya nufeshi, tun kafin ya karaso daddy ya daga mai hannu cikin tsananin tarin yace idan ka sake ka tabani Allah ya isa tsakani na dakai.


  kuka ya tsaya yanayi , baba yace kai haydar jeka kawai .


 cikin matsanan cin tashin hankali ya fita waje, wani haushin anas yaji yana taso mai, wai wace ma ya dauki hoton, duk shine yaja mai wannan tashin hankalin dana ke ciki, cikin zafin zuciya ya nufi mota yau anas saiya ci uban shi,zai gayamin uban waye yasashi ya dauki hoton


 

🕊🕊

Mmn Yazeed

           🕊🕊

[8:33PM, 4/22/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*




79 - 81



Kai tsaye gidan su anas ya nufah yana isa ya fito daga motar ko rufeta beyi ba, d'akin anas ya tura.


 anas naganin haydar abirke ce ya mike da sauri kafin ya bude baki haydar ya kaimai duka abaki, tuni bakin ya fara jini amman duk da haka bebari ba duka kawai yake aika mai , shiko anas yana dafe da bakin shi yake fadin haydar ka bari mana menene haka baka da hankali ko, mena maka, ganin da yayi haydar besan yanayi ba yasa ya fara ramawa.


 mahaifiya anas ce ta fito da gudu tsakiyan su ta shiga tana fadin kai kai ku bari menene haka kuma, kai haydar anas kubari, bazaku bari ba ko saina kira maza, basuma san tanayi ba gashi gidan babu kowa me gadin ma ta aikeshi dan haka ta fashe da kuka.


ganin mahaifiyar anas  na kuka yasa suka saki juna , da sauri haydar ya juya ya fita  momy nakira kai haydar zo nan , ina harya tada mota.



 yana shiga gida dakin ummi ya shiga ya sameta zaune kanta babu dan kwali ta kwanta akan kujera ta daga kanta sama tana girgiza kafah ga kuma hawaye nabin fuskar ta.


 jikin shi asanyaye yaje gabanta ya tsuguna ya rike kafar ta yace


  " ummi dan Allah kiyi hakuri ki yafe min, ummi kidaina zubar da hawaye akaina"



 cikin kuka tace haydar ka tashi kabani guri bana son ganin ka , dan ka bani mamaki kuma kabani kunya idan banyi kuka ba me kake son nayi, haydar ashe ka dad'e kana shiga kyauye kyauye kana lalata yaran mutane.


 cikin kuka yace ummi wlh ba haka bane itama wannan tsautsayi ne, momyn su ansa ce ta aikeshi gurin yayanta , shine yace narakashi, wlh ummi  muna kokarin shiga wauyen ne muka hadu da ita.


 da sauri ummi tace kaikuma dayake bunsuru ne baka gani ka bari KO, ashe shiyasa lokacin da salis yanuna yana sonta kaita tsoro da tsurfa kala kala, wlh haydar bakayi ba kayi asara wlh, ni kuma kasani takaici ka shayar dani bakin ciki , inama kai aka dauke aka barmin salis



kuka haydar ya fashe dashi sosai sannan yace kiyi hakuri ummi in Allah ya yarda zan zama kamar shi.


 cikin kuka ummi ke girgiza kai tana fadin bazaka taba zama kamar shi ba salis mutumin kirki ne , kwata kwata ba halin ku daya ba har yabar duniya bazan ce ga abinda yamin ba kai kuwa fah, tun kana karami kake batamin rai .


 yana kuka yana rokon ummi ta yafe mai amman ina daga karshe ma tashi tayi tabarshi agurin.


tashi yayi ya koma barayin su yaci kukan shi ya koshi gashi besan wanne hali daddy yake ciki ba.


 haka ya kwashe kwana biyu adaki dan ko sallah agida yakeyin ta babu ci babu sha duk yayi baki ya rame.



 ummi ma zuwa wannan lokacin tayi kuka harta gaji.


 

  daddy ne kwance a turakar sa yayin da alhj yusuf ke zaune agefen shi yana mai yajiki.


 ahankali daddy yace naji sauki yusuf, Ina fatima fah?


 fatima tana nan lfy tace agaida ka.


  dan murmushi yayi kadan sannan yace nagode.


  zuwacen ya sake cewa kaga abinda haydar yayi KO, ashe duk surutun da mukeyi kallon mu kawai yakeyi , ya maida mu shashatai.


 dan dukar dakai alhj yusuf yayi kad'an sannan yace toh ya za,ayi sai hakuri kawai, itama fatiman tana cen tana cigaba da haukanta wai ita sai dai ya sake ta, nace zama tayi tabari ne.


 cikin zafi daddy, yace ai indai ina raye mamana baza dawo dakin haydar ba, me zatayi da dan iska.


 alhj yusuf da sauri yace yaya dan Allah ka dunga gyara kalaman ka akan haydar kai fah uba ne, kuma ai wannan abun daya faru da ne yanzon ya natsu.


Hmmm haka kake gani.


*****


ranar da haydar ya cika kwana 4 adaki hankalin ummi ya tashi dan ko motsin shi bata ji



kasa hakuri tayi taje ta samu daddy domin ta sanar dashi halin da ake ciki.


 tana shiga tace alhj haydar fah bana ganin wucewan shi kuma na tambayi me gadi yace shima ya dade be ganshi ba.


 da sauri ya daka mata tsawa bana son na sake jin kin kiramin sunnan haydar a gidan nan idai kina son zaman lfy, hannushi ya kad'a sannan yace fita ki bani guri.


  tana kokarin fita daddy ya fara kwalawa taslim kira.


 lokacin da ummi ta zauna afalo taga wucewan taslim aguje zata gurin kiran daddy, zama tayi ta dafe kai.


 zuwa cen sai ga daddy ya fito taslim na binshi abaya ko sallama bema ummi ba ya fita abin shi, taslim ko zama tayi kusa da ummi.


 ummi juyowa tayi ta kalli taslim tace taslim tashi kije dakin haydar ki gani lfy yake.


 wasa taslim ta fara yi da yatsun ta sannan tace ummi daddy fah yace idan naje gurin yaya haydar be yafemin ba.


 da sauri ummi ta dafa kirji wato alhj abin har yakai haka afili tace au haka ya fad'a miki zumunci zai raba kenan toh  bazai yiyuba ainima ina da hakki akan ki, maza kije ki duba dan uwanki.


kuka taslim ta fara tana buga kafa asa tana fadin dan Allah ummi karku sani acikin wannan mgnr.


mikewa ummi tayi tana fadin kada Allah yasa kije ,fita tayi ta shiga dakin su haydar.


 makure ta sameshi akan gadon shi ya rufah da bargo, tana zuwa ta yaye bargon , kallonta yayi da jajayen idon shi, ya fara kokarin tashi.


ahankali tace baka da lfy ne?


  wasu safbin hawaye ne suka zubo masa sannan yace.


hakalina ne yaki natsuwa ummi damuwa yamin yawa saiyau nasan nayi rashi, ummi wlh nasan da ace salis na nan bazai gujeni ba kuma ko ya guje ne bazai wuce kwana daya ba, ummi dan Allah karki gujeni kizaman min kamar salis.


 da sauri ummi ta toshe mai baki tace ya isa ya wuce haydar

tashi kaje kayi wanka.


itako fatima yau tun safe take kuka tun da mahaifinta ya shaida mata ta shirya yau haydar zaizu su tafi gida.


 dan haka ta wuni tana kuka.


  4:15pm mama ce ta fito daga d'aki ta kalli Fatima tace


  " wai har yanzon kukan kike, menene naki na tada hankali tunda kema kisan abinda kk so ba faruwa zaiyi ba.


 cikin kuka tace mama tohni wai meyasa baki sona ne ,daga ke har baba naga baku damu da abinda haydar yamin ba bayan da har cewa kukayi idan kuka samu wadda yamin haka sai inda karfin ku ya kare.


  shiru mama tayi zuwa cen tace fatima dama wulakanci muke guje miki amman kinga tunda Allah yasa shine ya aikata babu wani wulakancin da zaiyi miki.


mama bata rufe baki ba fatima tace mama ai an mun wulakancin  tun yaushe ummi ke fadin dan nasamu za,arufamin asiri ba dama nace bana son haydar saita gayamin irin wannan mgnr kuma duk ranar da naga ummi saina gaya mata mgnr da har ta mutu bazata manta ba.


 cikin fada mama tace karki fara fatima ni bana son fitsara, ai ko baki ce mata komaiba ta daiji kunya, kitashi maza ki shirya anjima zaizo ku tafi.


  muryan hjy yadikko sukaji tana fadin babu inda zata indai ina raye bazata koma gidan haydar ba me ake da dan iska, ke Fatima taso muje.


tuni murna ya kama fatima da sauri ta dauki gyalenta tayi waje


 mama ce ta biyo bayan su tan a fadin hajiya dan Allah kiyi hakuri  babanta ya riga yayiwa haydar waya anjima zai zo ya dauketa.


 hajiya na kokarin shiga mota take fadin waye baban nata, shima zaizo ya sameni.


  da daddare haydar ya nufi gidan alhj yusuf ciki da farin ciki saidai yana isa mama ta shaida mai abinda ke faruwa.


  be firgita ba domin shi aganin shi kakar tasu kayan sauki ce batare da bata lokaci yayi sallama da mama ya wuce gidan.


yana sallama yaga hajiya zaune afalo, da sauri ta mike tana fadin waye nan, me ya kawo ka?


ahakali yace hajiya nine fah.


Eh ai nasan kaine mara kunya fitsararre, maza ka fitamin agida tun kafin nama uhu barawo.


dan murmushi yayi kadan ya zauna akujera.


 tana ganin ya zauna ta fara kira me gadi zoka taimake ni barawo ne ya shigo min.


 aguje me gadin ya shigo yana fadin ina yake.


  haydar na kokarin kwanciya akujeran yana fadin baba jeka abinka rudun tsufa ke damunta.


 cikin fada tace uwarka ce mahaukaciya mara mutunci kawai.


  dasauri haydar ya tashi ya zauna yace karki kara.


 idan nakara fah dukana zakayi?


nadai cemiki karki kara.


  cikin fada tace dan ubanka kai ba sa an yina na bane kaje ka turomin uwar ka dama ina da cikin ta.


   baza yayi da ita taita mgn ta gaji yaki kula ta dan yaga nema take tamai sharri.


itako hajiya  jinda tayi yayi banza yasa ta dauki wayarta no mahaifin haydar ta kira yana dauka ta fashe da kuka tana fadin kazo ka fitan min da d'anka daga gida gashinan yana neman duka na 


 


🕊🕊

Mmn Yazeed

             🕊🕊🕊

[6:38PM, 4/24/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*




82 - 84




Mikewa haydar yayi yana fadin lallai hajiya abin kuma harda sharri.


yana kokarin shiga dakin hajiya yana fadin kuma baki isa ki hanani ganin fatima ba.


  bayan shi tabi da sauri tana kai kai karka shigar min daki .


 yana sakai dakin yaga wayam babu fatima ya waiga gurin hjy yace Ina take?


 da saurinta tace tana gidan uwarka



Yana kokarin  bata amsa alhj yusuf shigo.


 da sauri haydar ya fara gaida shi hajiya ko tuni ta fara babatun tana fadin yauwa gara da Allah ya kawoka ka ganshi nan tun d'azon yake  min rashin kunya kamar zai gogi kafada dani.


  Shiru alhj yayi zuwa cen yace kai haydar tashi ka tafi .


 mikewa haydar yayi cike da takaicin tsohuwar kakar su ya so ace ta bari ko ganin fatima ne yayi haka ya wuce yanata hararan hajiya.


 hajiya ta kalle shi ta juya tana cewa alhj yusuf kana ganin Inda yake gallamin harara ko?


 dan murmushi yayi sannan yace hajiya ai ba me shiga tsakanin ki da haydar zaku shirya ne.


tana kokarin zama tace aini mun riga mun raba jaha, auren dama tuni tace banyi , itama fatima tace batayi sai akai kasuwa.


 shima zama yayi sannan yace hajiya hakuri za,ayi bawan da baya kuskure, kuma kinga yayi nadama.


ina sam bazai yuwuba haka kawai yariya yar karama da ita yaje ya dauko cutar zamani ya manna mata, babanshi da kansa ya gayamin kwanaki har gida aka biyo shi da cikin shege, dan haka idan ku baku damu da lfyr yarku ba, ni kubarmin inaso.


daidai lokacin daddy yayi sallama ya shigo, bayan ya zauna yace ina haydar din.


alhaji yusuf yace ai ya tafi tuni.


cizon lebe yayi sannan yace ai naso nazo na sameshi agidan nan , dana nuna mishi karyan iskanci yake, dan beda mutunci sai yaje yayi shaye shayen sa beje ya sauke akan mahaifiyar shiba saiya nufu tawa mahaifiyar.


  alhj yusuf ya bata rai sannan yace babu abinda yasha ai nazo na sameshi , shi neman matar sa yazo, dan ninamai waya yazo ya dauketa toh kafin yazo kuma ashe hajiya taje tafi da ita.


da sauri daddy yace da izinin wa zaka bashi matar tasa?


shiru yayi zuwa cen yace nidai nafi son ta koma dakinta dan zaman beda wani amfani.


daddy yana huci yace toh bazata koma ba, ko kanason ka nunamin karfin ikonka ne akanta, toh baka isa ba dole ne nayi iko da fatima kamar yadda zanyi da taslim, dan haka ninace bazata koma ba.



cikin fara,a hajiya tace Allah yama albarka.


shiko alhaji yusuf shiru yayi ranshi bace zuwa cen yace nidai alfarma nake nema dan Allah ayi hakuri abashi mat...... cikin fada daddy yace baza abashi ba idan kana iyawa kazo ka dauketa ka bashi.


 da sauri alhj yusuf ya mike ya fita fuuuuu.


duk suka bishi da kallo hajiya yadikko tace au fushin banza kai tayi komawa ne dai bazata yi ba.


 shima daddy be dade ba yayi sallama ya tafi.


washegari


alhj yusuf na zaune afalon gidan sa, yana labartawa mama abinda ya faru, bayan ya gama mata bayani, tayi shiru tana nazari.


zuwa cen tace alhj ajima zanje na ruki hajiya nasan data amsa daddyn su fatima shima zai sakko.


 da sauri yace a,a karkije yanzon kinayin mgn zasu fassara ta da wata munufa ninayi alkawarin bazan sake cewa ta koma ba, kuma shima haydar din zanbashi hakuri ga yanmata nan da yawa agari ya neme wata



shiru mama tayi ba dan ranta ya so ba, alhj yusuf na zaune agurin ya daga waya ya kira haydar ba,a  dau lokaci ba haydar ya iso bayan ya zauna ya mika gaisuwa.


 jiki babu kwari suka amsa, shiru sukayi na dan wani lokaci sannan alhj yusuf yace



  " haydar kasan dalilin kiran ka?


 cikin dasheshshiyar murya yace a,a.


 alhj yace akan mgnr ki da fatima ne, kasan daddyn ku ya dauki zafi akan mgnr dan haka nake son na baka shawara , ko da bani bani bane mahaifin ka amman nasan zan baka shawara ka dauka, dan haka inason kayi hakuri ka rubutawa fatima ta karda , dan na kula daddyn ku ya shirya daukan matakin da idan haka ta kasan ce bazakaji dadin rayuwar ka ba, sabo da bakin iyaye da kake gani babban masifa ne.


 'kasa yayi dakai ya kasa daguwa , ko motsi bayayi.


shima alhj shiru yayi zuwa cen yace haydar nasan mgn ta zatama tsauri da yawa, amman inason ka daure kayi haka din, idan Allah ya nufah zaman ku be kare ba sai kaga ta koma daga baya, kaje ka nemo ko yar waye ni zan tsaya maka ayi auren.


  a hankali haydar ya dago kai, idon shi cike da hawaye yace baba wlh ni babu wata wadda nake so fatima kawai nake so dan Allah baba karka bari daddy ya rabani da ita, nasan kai ka dai ne zaka iya tsaya min, karashe mgnr yayi cikin kuka.


shiru alhj yayi yana sauraran haydar sautin kukan shi kawai kakeji.


 

 mama ko tuni tausayin haydar ya kamata dan haka cikin sauri tabar wajen.


alhj yabita da kallo sannan ya juyar da kallon shi ga haydar yace


 " kai haydar ya isa haka, ya kake yin abu saikace ba namiji ba, karna sake ganin ka kana kuka akan fatima, fatiman me, ga yan mata cen birjik agari, ko hadu kake so sai ahada maka.


  ahankali haydar ya fara share hawaye zuwa cen ya mike yace na tafi.


  shima alhj asanyaye yace toh ka gaida mutan gidan.


har haydar ya isa gida kuka yake yi, kai tsaye ya dakin ummi ya shiga.


  ummi na ganin haydar ta dawo da baya ta zauna akan kujera sannan tace haydar dan allah ka kwantar da hankalin ka.


 cikin kuka yace ummi bazan iya ba, bazan iya rayuwa babu fatima ba kuma su daddy nema suke su rabani da ita, kuka yake sosai.


   hankalin ummi ya tashi ahankali tace haydar yanzon fatima tana ina?


  atakaice yace gidan hajiya.


 shiru tayi zuwa cen tace tashi muje gidan.





🕊🕊

Mmn Yazeed

            🕊🕊🕊

[6:12PM, 4/29/2017] Fadila Lamido: _©Exquisite Online Writers_


                  🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*




85 - 87



*SLM masoya wanna lbrn Tsuntsun me wayo, kunjini shiru kwana 2, haka ya faru ne sanadin ciyon kai da nayi, nasamu sakonnin ku na gaisuwa agereni babu adadi, kuma nagode da nuna kulawar ku agareni, wannan ya nuna min kuna biye dani kuma kunajin dadin wannan lbrn😍😍😍*





Haydar ne kejan motar cikin garaje dan ya balakin kosawa su isa gida.



ummi ta bishi da kallo tace haydar kajamu ahankali garajen me kake.


 bece komai ba yaci gaba da tafiya idon nan zuro zuro.


suna isa ummi ta sauka, har ta kusa shiga gidan ta waigo tace haydar kasan menene, ka zauna ka jirani na fara shiga zuwa anjima sai ka shigo.


Haka ya hakura ummi ta shiga badan ranshi yaso ba.


Lokacin da ummi tayi sallama afalon hajiya, ta hango fatima kwance akan cinyar hajiya, kibiya ce ahannun ta tana tsafewa fatima kai.


Ciki ciki hajiya ta amsa sallaman ummi fatima ko tana ganin ummi ta fara kokarin mikewa, hajiya tasa hannunta ta dan danne fatima sannan tace kwanta abin ki.


Bayan ummi ta gaida hajiya, sai shiru ya ziyarci falon.


Zuwa cen ummi taga shirun na hajiya yayi yawa, bayan tasan cewa surukar tata mutun ce me sakin fuska da wasa da dariya, amman yau tazo taga sabanin haka.



   Bayan ummi ta gama tunanin ta tayi kundun bala tace



   " Hajiya nazo ne akan maganar fatima da haydar"


Kan hajiya na kasa tana kokarin tajewa fatima kai, tace toh inajin ki, yaya akayi?



  Tace bawani abu bane hajiya daman hakuri nazo nabaki dan Allah kiyi hakuri komai ya wuce.


  Dariya hjy tayi sannan tace ashe baki da kunya haka ban sani ba, ai banzaci zakizo ki tareni da  mgnr haydar da fatima ba, kokin manta lokacin da kikecewa rufawa fatima asiri haydar zaiyi, saboda kawai tsautsayi ya fada mata, yazun badan Allah ya tona mai asiri ba, nan da shekara ishirin saikin goranta mata, kuma babu abin da yafi bani mamaki   duk abinda haydar yake yi baki gani, wai har kece kike bude baki kina fadin duk abun da namiji yayi ado ne, toh yaje ya karaci adon acen munan bamu bukata.



   Ummi jitayi kamar kasa ta bude ta shige sai yanzon ta gane be kamata ta biyewa haydar akan duk abin da yake so ba, cikin kuka tace


 " Hajiya tabbas nayi kuskure amman ina neman gafara dan Allah ki tayani bawa fatima hakuri ta yi haru ta yafemin.


Fatima dake kwance jikin hajiya ta kara matse idonta kamar me bacci.


 Haydar ne yayi sallama ya shigo, be ko kqlli inda ummi take ba, kai tsaye ya wuce gaban hajiya ya tsuguna yana leka fuskar fatima, hajiya bata ce komai ba, illa binshi da kallo da take.


  zuwacen ya daga hannu zaikai jikin fatima, muryar hajiya yaji tana fadin wlh ka taba yariyar nan saina barka kwance.

 

 Ko ajikin shi hancinta ya kama yadan matsa kadan


. zabura tayi da sauri ta mike tsaye cikin dakin hajiya ta nufa tana fadin Allah ya isa.


  tashi yayi zaibi bayanta sai alokacin ummi tayi magana cikin muryar da taci kuka ta koshi tace karka bita haydar , kayi wa fatima lefi yanzon neman gafarar ta ya dace kayi.


 daidailo kacin hajiya yadidko ta fitoh daga kitchen rike da wata yar karamar muciya tana fadin barshi ya bita idan ka fasa ka raina uwarka mara kunya kawai fitsararre.


 Juyawa yayi ya kalli fuskar ummi yasan lallai tayi kuka wani haushi ne ya taso masa ya juya ya kalli hajiya yace towai ke da kike wani shishshigewa yarkice..... 

ummi ce ta daka mai tsawa sannan ta mike tace muje


  Haydar na gaba ummi na binshi abaya suna kokarin fita ummi tace muntafi.


 ta bude baki zatayi mgn haydar yace kuma wlh zan dawo idai baki bani Fatima ba bazan taba daina zuwa ba

na dinga sintiri kenan.



har suka koma gida haydar cike yake da haushin hjy


ummi kuwa kalaman hajiya ne suka tsaya mata amakoshi, babu abin da yafi bata mamaki wai yau fatima ce taki gaisheta har tana wani bacci dan dai kawai karta gaida ta, taslim ce ta katse mata tunanin da fadin ummi kun dawo?


 Ajiyan zuciya ta sauke sannan tace mundawo taslim.


  taslim ta sake cewa ina fatima ai na dauka tare zaku dawo.


 Saida ummi ta share hawaye sannan tace ai fatima inaga saidai muyi hakuri domin fatima ta hada kai da hjy suna neman ganawa haydar azaba, saboda sun fahimci haydar ya kamu da son fatima, nima kaina bakiga yadda hajiya ta rufe ido tacimin mutunci ba, fatima ko,ko kallo ban isheta ba, bare nasa ran zata gaidani.


  Tuni taslim ta dafah kirji tace ummi fatiman ce tamiki haka, toh ai ba dole bane saita dawo, shima yaya haydar dinne ya cika naci ya rabu da ita mana.


 ummi tace ai haydar bazai iya ba yariga ya zama kamar wani wawa akan fatima, wlh tunda nake bantaba tunanin akwai yariyar da zata juya haydar haka ba, yaunzo fah ko mgnr fatima yakeyi babu wuya kiga hawayen shi. 


mikewa taslim tayi tace ummi aikuwa yanzun dai dole ne ya rabu da ita .


  suna cikin haka haydar shigo jiki asanyaye bayan ya zauna yace ummi wai yaushe alhaji babba zai dawo.


cikin daure fuska ummi tace


  " Ni ina zan sani ai wannan saidai ka tambaye daddyn ku ko kuma alhj yusuf dan nasan ko hjy yadikko batasan sanda zai dawo ba.



  Shiru yayi zuwacen yayi kwalkwal da ido yace toh ni yanzon ummi ya zanyi hakuri nafah ya fara karewa narasa ya zanyi, ummi dan Allah ki taimakeni mana.


  taslim ce ta bude baki ahankali tace 


  " toh yaya kaima dai kayi hakuri mana ka rabu da ita, tunda tace bataso ga yanmata nan ka neme wata mana.


  yadda taga haydar na kallonta ya sa tayi shiru tayi kasa dakai , mikewa yayi azuciye ya fara takowa kusa da ita, ummi ta mike da sauri ta shiga tsakiyar su, dan haka haydar ya fara fadin dan ubanki ina wasa dakene ni sa,an wasanki ne, daker ummi ta samu ta fitar dashi adakin.


   Kwanci tashi babu wuya yau fatima satin ta 5 agidan hajiya yadikko haydar yayi sintiri har yagaji dan haka haydar ya koma ruwa dan yanzon hargida yake kawo yan mata, ummi tayi mgn harta gaji kuma tayi tayi dashi ya nemo wata yaki gashi duk yayi wani iri yayi baki ya rame, dan haka ta yake shawaran zatamai aure ko yana so ko baya so.



Fatima ce kwance kan gadon hajiya yadikko sai sharara bacci take, hajiya ta bita da kallo tace


   " ke wai baccin nan naki na lfy ne kuwa"


mika tayi sannan tace hajiya gajiya fah nayi .


  da sauri hjy tace aikin me kikayi, zakice wani kingaji, toh kitashi ga iyayenki cen sunzo.


 fatima na kokarin tashi hajiya yadikko ta bita da kallo sannan tace.


   fatima anya baciki gareki ba kuwa, yaushe yabon ki da al,ada?


 cikin fatima ne ya bada wani tsurrrrrr saboda tsaban tsoro.


  hjy ta sake cewa bada ke nake mgn ba, budemin tafin hannun ki nagani.


  kara damke hannun ta tayi sannan tace hajiya dan Allah kibari, karki jamin bala,i ni bani da kome dan ko yanzon ma al,ada nakeyi





🕊🕊

Mmn Yazeed

            🕊🕊🕊

[8:25PM, 4/30/2017] Fadila Lamido: 🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*




88 - 90




Kallon ta hjy tayi shekeke sannan tace ke karki kawomin iskanci, bafa yau aka haifeni ba, batun yau na lura ba ciki gareki.


  hawaye ne ya fara zubowa fatima cikin kukan tace nifa bani da ciki haka kawai sai ki kalleni kicemin ina da ciki, ke likita ce, toh ko likita sai ya duba yake fad', karashe mgnr tayi cikin turo baki, sanan ta mike tayi falo.


 daddy ta gani tare da baban ta, daddy na ganin ta ya washe baki, yace mamana yayadai ko baki da lfy ne duk sanda naxo sai hjy tace kina bacci.


 yar dariya tayi sannan ta zauna tace lfy lau nagaji ne daddy, daganan ta shiga gaishe su daddy ne kadai ya amsa, amman alhj Yusuf yiyayi kamar bejita ba tare da kallon wani gefe.


 hajiya ta bishi da kallo, tace waikai kana nufin fushi kake da fatima, toh ai nima saika daina mgn dani tunda nina hata komawa.


  cikin sanyin murya yace toh hajiya ai wannan be kamata ba, tunda da haydar da fatima duk daya suke awajen ki, gashi nan yanzon duk kusa shi yazama wani iri duk ya bi yarame.



   da sauri hajiya tace yazama tsinken sakuce ma ni babu abinda ya dame ni, aishi ya daura wa kansa fita.


   daddy shiru ya musu bece kome ba zuwacen ya juya barayin fatima yace ke tashi ki kawo min ruwa.


 shiru yaji kanta na bisa hannun kujera kwace.


  ya sake cewa fatima dake fah nake.


nan ma shiru, hajiya ta juyar da kallonta ga fatima sannan ta mike tana fadin bari na kawo maka, ita fatima yanzon inda kasan kasa haka takoma.


zuwa cen ta dawo dauke da ruwan tana cigaba da fadin kunga wannan baccin tun asuba takeyin sa, yanzon haka ko sallar azahar batayi ba, data bude ido zata sake mayarwa.


 cikin ta kaice alhj ya mike ya nufi fatima yana fadin kuma kika barta ai wannan iskanci ne ga la,asar na tahowa, daidai lokacin daya zafga mata rankwashi.


da sauri ta mike tana rike da kai take kallon su, cikin fad'a yace maza kije kiyi alwala kizo nan kiyi sallah.


 wucewa tayi sumi sumi zuwacen ta fito sanye da hijjab, gefen hajiya ta shinfida sallaya, tana idarwa kuwa ta shige cikin hijjab din taci gaba da baccin ta.


wannan karon daddy ne yayi mgn yace hajiya wai waccen yariyar baccin nan nata na lfy ne kuwa, jifah saikace wata yar maye.


 alhj yusuf yace kashhh kayi shiru kawai jira nake na tashi na bugata da bango.


  cikin sauri hajiya tace a,a a,a karka fara, kana son kajawo mana bala,i kenan, kubarta tayi baccin ta wannan baccin nata me daliline dan ko tatama banayi ciki gareta.



  shiru sukayi kowa da abinda yake sakawa zuwacen daddy yace amman hajiya ya kamata akaita asibiti dan atabbatar da haka.


 hajiya ta kalli alhj yusuf tace toh ko kai zaka kaita?


  da sauri ya mike yace wa, Allah ya kiyaye ai mijinta ya kamata ku kira bani ba, waje ya fito cikin shi cike da dariya, dan wannan mgnr ba karamin dadi tamai ba.


hajiya kuwa alhj na fita tabi bayan shi da harara sannan ta mike tace ni bari naje nakaita.


 daddy ma mikewa yayi yace toh ki tasheta saina kaiku.


haka ko akayi suna zuwa bayan yan gwaje gwaje likitan ya shaida musu tana dauke da cikin sati 6.


 ranar daddy ya koma gida cike da farin ciki wanda ya kasa boyewa, yana kokarin shiga gida ne suka hadu da haydar zai fita, ya dan rusuna ya gaida shi.


 amsawa yayi sannan yawuce, abin kuwa yabawa haydar mamaki dan tunda abun nan ya faru daddy baya amsa gaisuwa shi, dan haka haydar ya shiga tatama kodai daddy be ganeshi bane dan yaga kamar arude yake.


    ******


ummi na zaune ita da taslim acikin dakin ummi, shiru sukayi kowanne cikin su da abinda yake sakawa itako ummi tunanin mijinta ne fal azuciyar ta, sabo da tun da abun nan ya faru baya mgn da kowa agidan sai taslim , acewar sa ita kadai ce take mishi biyayya.


  itako taslim haydar ne ya hanata sakat agidan daya ganta neman dukanta yakeyi dan gani yake taslim munafuka ce bata son farin cikin shi , dan yaga almar harda ita ason ya rabu da fatima


suna cikin haka sukaga anturo kofar da sauri ummi ta kalli gurin dan zatonta haydar ne, baki ta saki tana kallon daddy shima ita yake kallo fuskar shi cike da murmushi , zama yayi bakin gadon, dan haka taslim ta gaidashi tamike ta fita cike da mamaki dan tunda take da wayon ta bata taba ganin daddy adakin ummi ba sai yau.


  itako ummi dadi taji bakadan ba, amman saita dake ta buye farin cikin ta ahankali tace lfy kuwa?


 d'an murmushi yayi sannan yace waike bakisan ina fushi dake bane , bazaki iya zuwa ki bani hakuri ba.


tace lefin me namaka kawai dai lefin haydar ne ya shafeni, kuma ni bani na turashi ba, kuma nima abin ai bemin dadi ba.


  d'aga hannu daddy yayi sannan yace ni bawannan ne ya kawo ni ba, albishir nazo na miki.


  ummi tace to ijinka.


  daddy ya sake cewa amman fah zaki bani tukuici.


murmushi tayi sannan tace indai ya cenceci abaka ai sai nabaka .


saida ya cire hular dake kansa sannan yace  fatima nadauke da ciki.


  farinciki ne ya rufe ummi nan da nan tace alhj da gaske?


  shima yana dariya yace zan miki da wasa ne, daga nan ya shiga labarta Mata yadda akayi.


 tace  kai naji dadin wanan lbrn anjima zan baka tukuici🙈


 da daddare ummi zama tayi tana jiran haydar ya dawo tamai albishir amma har bacci ya kwasheta be dawo ba.


 sai 12:15 na dare ya dawo kai tsaye dakin sa ya nufah domin yu tun safe cikin sa ke ciyo kuma yasan bawani abu ke damun saba illa sha,awa dake damun sa, ko yau ya fita ne da niyar ya samu wacce zata biya mai bukata, amman ga yan matan yana gani ya kasa amfani dasu kusan yan mata 5 ne suka neme su kebe dashi, saiya tafi da niyar yayi saiya kasa, dan haka ya tattara ya dawo gida.


  kwace yake yayi daidai akan makeken gadon sa dagashi sai garen wando, wani irin zafi yakeji amarar shi, murkusu yaitayi zuwa cen yaji numfashin shi na neman daukewa dan haka ya fara neman no alhj yusuf, yana dauka yace 


    " baba kazo ka kaini asibiti zan mutu"

 abunda ya fada kenan ya kashe wayar, salis ne ya fado masa arai, dan da ace yana nan bazai galabaita haka ba, zai taima ke shi, koda kuwa ba gida daya suke ba, nan danan ya fara kuka.


bayan mintinan da bazasu wacce 30 ba alhj yusuf yazo ya dauke shi suka nufi asibiti, cike da bacin rai.


karfe 8:00 na safe suka baro asibitin alhj yusuf ne kejan motar yayin da haydar ke zaune agefen shi.


lokacin da suka kusa karasawa gidan daddy ne alhj yusuf ya tsaya ya kira no mahaifin su alhj salisu, bayan ya dauka ya fara gayamai matsalar haydar da fatima komai ya gaya, cikin da fatima ke dauke dashine kawai be fad'a ba.


bayan ya gama sauraran shi yace Ku saurareni ina tafe acikin satin nan.


kashe wayar yayi sannan suka karasa gidan daddy.


duk suna zaune afalo, sukaji sallaman alhj yusuf tare da haydar suka shigo.


  daddy ya kallesu yace daga ina haka?


cikin takaici alhj yace dole ku tambaya tunda kun kwanta hankalin Ku kwace kubar haydar cikin halin rashin lfy, badan Allah yasa yayi dibara ya kirani ba kila da saidai ya mutu.


murmushi daddy yayi sannan yace toh me d'a tunda Allah yasa kai yaga mahimmancin ka ya fada ma aishi kenan, ai yasan damu agidan amman be nememu ba, juyawa yayi ya kalli haydar yace meya sameka?


 cike da mamaki haydar ke kallon daddy, ya kasa furta komai yayi, mamakin sakkowan daddy yake.


 ummi ta sake cewa dakai fah ake mgn.


 daker ya bude baki yace ciwon ciki ne.


  shiru ummi tayi tana nazari, muryan daddy taji yana tambayan haydar daman yana ciwon ciki ne?


 murya ciki ciki yace Eh.


 shuru ne ya ziyarci falon, zuwacen alhj yusuf yamike yayiwa ummi sallama ya fita, daddy ma mikewa yayi yabi bayan shi.



suna fita ummi ta dube haydar tace toh yajikin?


 "yace yayi sauki"


ummi ta sake cewa jiya inata jiranka kadawo nama albishir, har nayi bacci baka dawo ba.


 da sauri ya waigo yace ummi daddy yace naje na taho da fatima ne?


  itama cikin sauri tace a,a bece ba amman dai fatima nada ciki.


  mikewa yayi da sauri ya dungule hannuwan shi yace yesss thank God, komawa yayi ya fada kan kujeran da karfi


 ummi kallon shi kawai take tana murmushi.


  ganin inda ummi ke kallon shi, sai kunya ya kama shi, yana sosakai yace ummi kiyi hakuri mantawa nayi kina gurin.


  mikewa tayi tana fadin a,a kayi abinka ai zamani ne.


  tana wucewa shima ya mike jiyayi yajishi garas, yanzon dole abashi matar shi , dan haka motar sa ya shiga har ya zauna yaji alhj yusuf na kwalamai kira da sauri ya sakko ya nufi gurin da daddy da alhj suke zaune.


  tsugunawa yayi agaban su yace gani.


  alhj yace toh kaida baka da lfy ina kuma zaka, banson yawace yawace fah


  keya ya fara sosawa sannan yace gidan hajiya zani.


  shiru yayi sannan yace toh saika dawo.


itako fatima tunda suka dawo daga asibiti take kuka' hajiya tayi tayi da ita tayi shiru taki ahaka suka kwana, kuka harda majina.


  ganin inda hankalin ta duk yabi ya tashi yasa hajiya ta fara tunanin karfa damuwan fatima yasa  cikin ya zube, idan ko haka ya kasance bazataji dadi ba, domin suna da bukatan yara, dubara ce ta fado mata, dan haka ta dafa fatima tace


   haba fatima daga cewa kinada ciki saiki tada hankalin ki, idan kina tunanin za,ace saikin koma gidan haydar ne saboda kinada ciki to ki kwantar da hankalin ki, bazan taba bari ki koma gurin sa ba.


  cikin kuka tace ni dai so nake kawai aciremin cikin, haka kawai ina zama na za,ace wai wani ciki gareni.


  zaro ido hajiya tayi sannan tace fatima kina hauka ne, toh daga yau karna sakejin zancen zubar da ciki abakin ki idan ba hakaba kuwa kwanan nan zamu raba jaha

angaya miki nima bani da hankali ne kalanki ,kaga min yar banzan yariya, ta inda hajiya take shiga batanan take fitaba.


   cikin sauri fatima ta mike cike da haushin hajiya daki ta shiga, zuwa cen saigata ta fito sanye da hijjabi hannun ta dauke da akwati.


 cikin fada hajiya tace ina zaki?


  turo baki tayi sannan ta share hawayen dake kan fuskarta tace toh haka kawai sai kitayimin masifa, ni gidan babana zan koma.


  da sauri hajiya ta mike tace kinci bantan ubanki




🕊🕊

Mmn Yazeed

             🕊🕊🕊

[6:42PM, 5/1/2017] Fadila Lamido: 🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*




91 - 92




Ke wacce irin yariya ce da babu damar a gaya miki gaskiya, dan uban ki Allah ya miki kyauta kice maki so, bayan kina gani ba yawa gareku ba, naso ace na haifi yara da yawa amman Allah be yarda ba, guda 2 ya bani, nayiwa Allah godiya kuma naita addu,an ta sanadin biyun nan zamuyi yawa, toh gashima yanzon suma ku uku kawai kuka rage musu, kuma idan Allah yaso ku ukun nan sai kuntara mana uguwa guda



 cike da haushi fatima ta kalle ta tace caff dayake ke za,abarwa gadin duniya.


  itama hajiya cikin fad'a tace to ai saikizo ki karasa ni.


  dariyar haydar sukaji daga bakin kofah duk suka maida hankalin su gurin shi.


  har yanzon dariya yake yi hannuwan shi cikin aljihun shi, zuwa cen ya tsagaita da dariyar ya fara takowa cikin falon ya zauna sannan yace 


  yau dai na ganku arana har kun gama kule kulen naku?


hajiya ta kara daure fuska kai bana so shashanci ni nake maka kule kulen?


  toh hajiya idan ba kule kule ba ya za,ayi daga abu ya faru ki wani kanai naye kita zuga yariya, ya juya barayin fatima yace yi hakuri fatima zo ki zauna ni zan miki duk abin da kike so, badai cikin kike so araba ki dashi ba, toh karki damu, ta shi yayi ya isa gabanta ya rike akwatin sannan yace wannan bawata Matsala bace, yanzun kizo muje na kai ki asibiti


   bige hannu shi tayi ta saki akwatin ta koma daki tana share hawaye.


  cikin sauri yabi bayanta, hajiya ko ido kawai tasa musu.


  yana shiga ya sameta ta kwanta tayi rufda ciki, bakin gadon ya zauna yasa hannun shi ya dago ta



duk da kokarin kwacewan da yake besa ya saketa ba saima kara matseta da yayi  a jikin shi yana kai mata sunba, tun tana kwacewa har ta gaji tayi lakwass ajikin shi, dan ta gane wahala kawai zatasha bazata iya kwatan kanta ba.


  zuwa can ya saurara mata ya bude baki ahankali yace 


  fatima dan Allah kiyi hakuri ki yafemin nasan na miki laifi, ina rokon alfarma ki yafemin ki dawo gareni, ki daina biyewa zugar hajiya rudun tsufa ne yake damunta, kara kwatar da murya yayi yace fatima idan kika amince kika dawo gareni zan nuna miki son daba kowane namiji bane zai iya nunawa matar sa, ko kuda bazan bari ya tabaki ba.


 tuni hawaye ya fara zubo mata domin kaman  haydar ya tuna mata da salis, shima haka yake fada.


  cikin kukan take fadin wlh bazaka iya ba, dan ko yaya salis daya fadi haka gashi ya tafi ya barni, naso ace yana nan asirinka ya tonu, da kaji kunya.


 cike da takaici yace fatima har akwai wata kunya da ta wuce wadda naji yanzo kowa fah acikin dangin mu yasan halin da muke ciki, hatta taslim karamar kanwata ta daina girmamani , kuma da kike mgnr salis, wlh  ni nasan da salis na nan shine mutun na farko da zai fara gafarta min, nasan zaiji tausayi na kuma zaiyi kokari yaga ya fitar dani daga cikin kunci, dan haka ina rukonki albarkacin son da kikeyiwa salis kiyafe min.


   kuka take sosai dan haka ya jawota kan kirjin shi yana fadi Allah yajikan salis, Allah ya gafarta masa ubangiji Allah ka haskaka kabarin sa.


  cikin kuka fatima ke amsawa da ameen ameen, dan haka ya kara matseta kamar zai sakata ciki.


   saida suka kwashe kusan minti talatin ahaka, sannan fatima ta daga kanta ta fara share hawayen, cikin ido ta kalli haydar tace


   kace duk abinda nake so zaka min ?


  da sauri yace eh

me kike so ko menene ki fadamin.


  cikin sauri tace toh cikin za,a cire min.


  shiru yayi zuwacan yace to shikenan gobe zan zo na dauke ki, kamar karfe na zanzo?


    tace ko da yaushe ne amman dai da wuri zaka zo .


  mikewa yayi tare da fadin angama ranki ya dade, sannan ya zuba hannu cikin aljihu yace to zan wuce baki ce nagaida kowa ba.


  dan ya mutsa fuska tayi sannan tace nidai inajiran ka, kazo da wuri.


  shima murmushi yayi sannan yace toh saikin ganni.


    

  yana fitowa ya kalli hajiya dake saune afalo yace duk d'an bakin ciki sai dai ya mutu.


  yana fita hajiya tayi murmushi tace ja iri.



   cike da farin ciki ya koma gida, washegari kuwa 9 agidan hajiya tamai, lokaci fatima na bacci saida yajirata tashi, tana bude ido kuwa ta fito falo da niyar tambayan hajiya ko haydar yazo, tana fitowa kuwa ta ganshi  zaune kusa da hajiya, cikin sauri ta koma ta dauko gyale ta fito tana fadin muje.


  saida hajiya ta kalli fuskar haydar sannan ta kalli ta fatima tace ina kuma zaku.


  haydar ne ya mike sannan yace ina ruwan ki.


  itama hajiya mikewa tayi sannan tace babu fah, amman dai fatima anyi wayon banza.


   basuce komai ba suka bar gidan.


   koda sukaje asibitin haydar ne kadai ya shiga zuwacen yaxo ya kira fatima.


  bayan ta zauna agaban likitan ya juyo gareta ya fara mata bayani madam mijiki ya riga  yamin bayani , zan baki magani amman kisani komai yana bukatar sirri, ki kama bakin ki karki gayawa kowa, dan maganin dazan baki yana da kyau bakowan ni asibiti ake samun shi ba, idan kika sha maganin ta fitsarin ki cikin zai fita, saidai maganin yana da duko ki.


  sosai fatima ta maida hankalin ta gare shi.


yaci gaba da cewa kadan daga cikin ka idojiji sune cin abinci akan lokaci, ba,aso meshan wannan maganin na zama cikin damuwa

sannan idan zaki kwata bacci ki kwata ta gefe dama ko hagu idan kika kiyaye wad'annan dukokin ko kwana 1 baza ayiba zaki fitsarar dashi.

   

mika mata manin yayi sannan yace koda cikin ya fita kuma badaina shan maganin zakiyi ba idan ya kare saiku dawo na cenza muku wani, dan idan kina shan maganin bazaki dauki ciki ba sai ranar da kika daina shan maganin.


godiya sukayi sosai sannan sukayi mai sallama suka tafi



suna cikin tafiya haydar ya kalli fatima data zauna tayi shiru, yace fatima tunanin me kikeyi, kina son cikin ya fita da wuri kuwa?


   inaso mana ai insha Allahu yau zai fita, shiru sukayi zuwace fatima ta sake cewa yaya haydar daman kai baka son yara ne?


  daidai lokacin dazai karya kwanan gidan hajiya yace


ina so amman ba yanzun ba.


  tabude baki zata sake mai wata tambayar taji yana fadin toh fah alhaji babba yadawo.


  tana daga kaikuwa taga jerin motocin dake gaban su, ta tabbatar eh lallai alhaji salisu ne ya dawo






🕊🕊

Mmn Yazeed

            🕊🕊🕊

[8:59PM, 5/2/2017] Fadila Lamido: 🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*




93 - 94




Kusan tare suka isa gida, alhj babba na saukowa a mota suma suna fitowa, cike da fara, alhj ke kallon su, bayan sun shiga gida cike da anna shuwa alhaji salis ya zauna yaran shine guda 2 agaban shi gefe kuwa ummi ce da mama duk sunzo taryan sirikin su,

 

  hardar da fatima ma suna zaune akasa, taslim ce kawai ta shige dakin hajiya ta boya domin yanzon basa zama inuwa daya da salis.


   abinci aka baje kowa yaci ya koshi har fatima sake jiki tayi taita tura abinci, duk da cewa bason ci take ba.


bayan sun kammala ne kakan su alhj salis ya shiga tattaunawa da  iyalan shi, haydar Allah Allah yakeyi yaji an sako zancen su da fatima.


  zuwa can alhj yusuf yace baba bakace komai ba akan mgnr haydar da fatyma.


dasauri alhj salis ya maida kallon shi  gare su yace ai na dauka kun gama komai, kuna nufin yanzon ba daga gidan su , suke ba, toh me kuke jira.


  hajiya yadikko tayi caraf tace ai alhj bazata koma ba, sakin ta zaiyi idan Allah ya sauketa lfy tayi aure.


  cikin sauri alhjn yace da wani dalilin, ai bazai yiwu ba wannan auren da kuke gani ko bayan raina ban yadda arabashi ba, abun da ya faru ya riga ya faru, gashi har ma naji kina cewa ansamu rabo.


 duk shiru sukayi suka samusu kunne.


  zuwa can hajiya tace alhj kana nufin duk rashin kunyan da haydar yayimin yace bulusss kenan, wacce kalma ce be kirani da ita ba, har fah habaici yake min, ko dazon saida ya kalli cikin idona yacemin duk dan bakin ciki saidai ya mutu.


d'an murmushi yayi sannan yace yamin daidai daya fad'a miki haka, yaga zaki kwace mai mata, ya juya ya kalli haydar daya dukar da kansa kasa yace


  kai ka tashi ka dauki matar ka ku tafi gida, idan kana da hankali wannan kadai ya isheka ishara.


  cike da farin ciki haydar ya fara godiya, fatima ta dago fuskarta cike da hawaye, hararar da alhj yusuf ya zafga mata yasa ta maida kanta kasa.


   haydar kuwa tuni ya mike yaje gaban fatima yace tashi muje, ko saina d'aga ki?


 hajiya ce tace to kuji irin rashin kunyar tashi ko.


 cikin dariya alhajin ya kalli hajiya yace haba fatima me yasa kikeyin abu kamar wacce rikicin tsufah ya kama, me yakai kunnen ki gurin su.


shidai haydar tunda fatima ta mike tayi waje be tsaya jin me suke tattaunawa ba,    

haka suka isa gida saikace kurame, fatima ko jifi jefi tana share hawaye.


 suna shiga barayin su ta ganshi duk yayi kora duk da batajin kwarin jikin ta haka ta zage tashiga gyara gidan tana hawaye, shima haydar be zauna ba tayata ya shigayi.


  zuwa can haydar yace wai fatima kukan me kikeyi inace mun riga mungama mgn, hannusa yasa ya riketa yace kibar aikin zan karasa, kije kiyi wanka sai kizo kisha maganin.


   bayan fatima tayi wanka tasha magani nan bacci ya kwasheta batare da tasan lokacin ba, haydar kadai ya karasa aikin dan haka lokacin da ya   fito wanka shima nan kusa da fatima ya kwanta gani yayi baccin nata yayi nisa dan haka ya dago kanta ya daura akan kirjin shi yasa hannun shi duk biyun ya zagaye ta


Sun dade ahaka gabadayan su bacci suke shararawa 


 su ummi kuwa sai yamma likis, suka dawo ita ma yau cikin farin ciki take dan haka suna dawo wa ta shiga kitchen domin daura abincin dare , tare da taslim sukayi komai suka gama.


 sai kusan 5:59pm haydar ya farka yayi mamakin gudun lokacin, ahankali ya fara tashin fatima, ahankali ta fara bude idon, bata gama was tsakewa ba taji wani fitsari ya kulle mata mara dan haka ta tashi da sauri tayi toilet.


  aguje haydar ya bita fitsari ya samu tana yi, saboda yadda fitsarin ya matseta har wani lumshe ido take.


  haydar na rike da kofar yana kallon ta zuwacen yaji tace Alhamdulillah yaya haydar ka gani cikin ya fita.


   dariya ce taso kwace mishi daker ya iya daurewa, yaje ya dagata yana fadin sannu fatima, har wani langabewa take wai ita adole ga me mara lfy


   cikin haydar cike da dariya har suka fito falo, kan kujera ta kwanta tace toh kaje ka gayawa su ummi.


  daure fuska yayi sannan yace kin manta abinda likita yace, ko bakisan komai da sirri yafi ba.


  turo baki tayi sannan tace toh idan sukaga ban haihu ba fah.


   yace babu ruwan ki ,kibarni ni zansan yadda zanyi nagaya musu.


    ********


  washegari da daddare haydar ya shiga dakin fatima cikin shigar da fatima keson gani zama yayi kusa da ita sannan yace fatima ya kamata ace zuwa yanzon musan abinda muke yi , ya kamata mugyara zaman mu, mudunga sauke hakkin junan mu, muyi zama naso da kyauna, bana umarni ba.


   ahankali ta daga idon tace waye zai so ka yayama za,ayi naso yaya salis sannan kuma naso ka.


  fuskar shi daure yace fatima ki daina yaudaran kanki, kuma ni banason kinamin maganar salis indai ba addu,a zakiyi mai ba,  matata ce ke, kuma nina san kina sona yaudaran kanki dai kawai kikeyi.


  cikin rashin kunya tace aiko baka isa ka hanani zancen yaya salis ba ina ruwan ka.


  azuciye ya mike har yakai bakin kofah ya tuna matsanan ciyar sha,wan daya kwana da ita, dan haka ya fara takowa ahankali ya dawo gabanta ya tsaya,




kome ya tuna kuma saiya koma.


yana fita fatima taja tsaki ta gyara kwaciyar ta.


 shiko haydar cike da tunani ya koma dakin sa, tunanin fatima ya shigayi yana son su kasan ce amman ya rasa ya zaiyi shiru yayi , zuwa cen wani tunani ya fado masa dariya yayi sosai sannan yace azuciyar shi, akan me ma zan damu kaina akan fatima yariyar da ba wayo gareta ba, dariya yakarayi daya tuna fatima wai har murna take, tayi fitsari ciki, dariya yayi sosai har yana rike ciki sannan ya fesa turare ya nufi dakin fatima cike da kwarin guiwa, dan yasa yiwa fatima wayo bawani abin wahala bane






🕊🕊

Mmn Yazeed

            🕊🕊🕊

[8:52PM, 5/3/2017] Fadila Lamido: 🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*



95 - 96



Lokacin da haydar ya shiga dakin fatima samunta yayi tana bacci kuma dagani tanajjin dadin baccin dan haka bazai iya tashinta ba.


 Ahankali ya hau gadon daf da ita ya kwanta ya manne da jikinta, zuwa cen yasa hannu ya rugumota jikin shi, yaso ya hakura ya barta tayi baccin ta Amman ina bazai iya ba, hannun shi ya fara wasa dashi ajikin ta.


   da sauri tasa ahanun ta tarike nashi ta tura hannun nashi baya sannan  tace yaya meye haka?


 Hannun shi ya Kara daurawa ajikinta ahankali yace dan Allah fatima kiyi hakuri ki bani hakkina, wlh amatse nake.


  da sauri ta tashi ta zauna tace nidai gaskiya kayi hakuri bazan iya ba.


 Shima tashi yayi ya zauna yace bazafah ki iyaba kikace , ko bakisan hukuncin matar da mijinta ya nemeta taki amince bane?


  da sauri tace nasani aini bani da lfy ne, kuma ni ina ganin kamar ma cikin be fita ba, dan duk abinda nakeji ban daina jiba, har yanzon.


  Daure fuskar shi yayi  sanna yace ya fita mana toh ya za, ayi ki daina ji, bayan har yazon mgni kike sha, hannun shi ya kara kaiwa jikinta yace fatima kiyi hakuri mana amatse nake kuma inada matsala idan kk hanani cikina zai iyayimin ciwo.


 Mikewa tayi ta fara buga kafa, tana fadin nidai gaskiya ka rabu dani bacci nakeji.


  Abin da fatima bata sani ba wannan abin da take kara riketa haydar takeyi.


  Zuba mata ido yayi kamar me kallon TV

ganin da yayi ya fara shiga yanayin da indai fatima ta hanashi zai iya shiga Matsala, dan haka muryar shi ciki ciki yace toh ya isa haka, na hakura , zoki kwanta.


 Cigaba tayi tana fadin toh kazo ka tafi dakin ka mana.


Daure fuska yayi sannan yace anan zan kwana, kuma wlh idan kika batamin rai, dasafe zanje nagayawa baba abin da kk min.


   Tanajin ya fadi haka ta tsaya cek kamar me tsonron kar wani abu ya kamata ta fara hayowa gadon nesa dashi ta kwanta, ba dadewa kuwa bacci ya kwasheta.


  Cen cikin barcin ta tafarjin nishin haydar wasa wasa taji abin na kara yawa , dan haka ta bude Ido ganin shi tayi cen gefe ya kudundune yana rike da ciki, dasauri ta matsa daf dashi tace yaya menene ?


  babu amsa sai wani irin numfashi daya ke fitarwa gawani uban zufah dake karyo mishi, kalmar shice ta fado mata idan kika hanani cikina zai iyamin ciwo.


  Kallon shi tayi sosai sannan tace ciyon cikin ne?


Hawaye ta fara gani suna zubo mishi, yana wani irin kamar numfashin shi zai dauke, dan haka itama kuka ya kwace mata, acikin kuka take fadin bari nakira ummi.


 Da sauri ya rike hannun ta yana girgiza mata kai, kuka take sosai domin abun ya balakin bata tsoro.


Cikin sauri takai hannun ta kan cikin haydar gurin dataga yana rikewa ta ture hannun shi tanayin kamar yadda taga yanayi, hawayen ta na sauka akan ruwan cikin shi.


Sun dade ahaka daga cen ta fara jin kamar numfashin na sauka  ahankali, dan haka ta gyara zamanta sosai ta dauki kanshi ta daura akan ciyar ta, taci gaba da abin da take.


Zuwa can taga bacci ya dauke shi dan haka ta bishi da kallo gani tayi harya fada yayi zuro zuro.

dan haka ta fajin haushin kanta dan ta dau hakkin haydar.


Ahaka fatima ta kwana bata runtsaba dan gani take kamar data cire hannun ta zai tashi, kiran sallan subahi ne ya tadashi, da sauri ya miki ya kalli fatima, da sauri ta dukar dakai, yace fatima bakiyi bacci ba, baki da hankali ne?


Kanta akasa tace banajin baccin ne.


 Shiru yayi sannan yace toh tashi kiyi sallah saiki kwanta.


Wanka yayi sannan ya wuce masallaci bayan ya dawo ya samu fatima zaune akan sallaya, wuceta yayi ya isa bakin gadon ya fara gyarawa, da sauri fatima ta miki ta rike zanin gadon.


Haydar yace sake mana zan gyara miki ne saiki kwanta.


Tace kabarshi zan gyara da kaina.


Yace a,a nizan gyara  

 Sakimai tayi dan yanzun batason yimai musu

 

Yana gamawa yace toh zoki kwanta.


Kokarin cire hijjab takeyi dan haka haydar ya nufi fita.


Harya fara tafiya fatima takira shi ahakali tace yaya.


  Dawowa yayi ya tsaya yana kallon ta kanta akasa tace ya jiki?



Murmushi yayi sannan yace naji sauki.


 Yana kallon fuskarta yaga hawaye na zubowa.


Hannu yamika ya kawota jikin shi yace meyasa kike kuka ?


  Cikin kuka tace dan Allah kayi hakuri ka yafemin jiya na jawo maka......hannun shi yasa ya rufe bakin ta sannan yace karki damu ai dama cen inayi, kitaya ni rokon Allah, ya yayemin.


tace eh amman dai ai nice sanadi, tunda ka fad'a tun kafin hakan ta faru


dariya yayi sannan yace toh naji ya wuce yanzon kije ki kwata, inason zaje na shirya kinga lokaci na wucewa.


   haka fatima ta wuni da tunanin haydar dan gsky ba karamin tausayi ya bata ba zama tayi tai tagume tace a zuciyar ta toh yanzun da haydar ya mutu ya rayuwa ta zata kasance, afili tace Innalillah wa ina ilaihir raju,un.


haka taita tunani daga baya ta wuce dakin ummi acen ta wuni har yanma ita da taslim.

.

shima haydar daya dawo barayin ummi ya shiga sai dare ummi tace su tafi dakin su.


  fatima bata jira haydar ba gaba tayi tana shiga ta fada toilet wanka tayi ta gyara jikin ta.


  zama tayi tana jiran shigowan haydar amman har kusan 10:30 be shigo ba , zuwa cen taji motsin shi afalo dan haka ta mike, ta dauki karamin hijjab dinta ta saka ta nufi falon .


koda ta fito falo baya nan, dan haka ta nufi dakin shi, sallama tayi ta turo kofar yana kwance akan gado yana danna waya, ya dago ya kalleta ya saki murmushi.


  Alama yayi mata da tazo ta zauna a gaban shi, tana zama ya jawota jikin shi ya rungume dan bakaramin dadi yaji ba dayaga ta kawo kanta da kanta.


   *******


washegari fatima sai  kusan sha biyu na rana ta fitoh dakin haydar, kwana 1 kawai da tayi adakin haydar harta fita hayyacin ta , tun daga wannan ranar fatima bata sake yinkurin hana haydar hakkin sa ba, koda sonawa zai nemeta bata hanashi, saidai idan bayanan ta zauna taita kuka, kuma dataji dawowar shi gabanta ke faduwa.


 ahaka har suka kwashe wata 5 fatima sai ramewa take,gashi al,adanta shiru har yanzon, kuma cikinta nata kara kunbura harda wani motsi yake , bata manta lokacin da tacewa haydar har yazun fa al,dan ta be dawo ba kuma gashi cikin ta sai girma yake , kodai cikin be fita bane yana nan, amman sai yace mata ya fita mana ,ai kece bakishan magani akan lokaci shiyasa yake kumbura miki ciki ,nan gaba ma har mutse zai dinga miki.


tagumi tayi tana kallon cikin zuwa cen ta fara tuno lokacin da haydar ke  magana saitaga kamar yanayi ne yana boye darigar sa, dan haka ta fara tunanin anya kuwa ba wayo suka shirya mata ba, hanya kuwa ciki yana fita ta fitsari, afili tace koda yake likitan yace sabon magani ne, toh amman meyasa cikina yake girma kamar na me ciki kuma meyasa yaya haydar yake boyewa yana dariya, mikewa tayi tare da fadin nasan abinda zanyi.



    barayin ummi ta nufah acen ta samu haydar dan haka ta wuce dakin taslim, ta bar haydar da ummi suna hira .



   Tana shiga samu taslim zaune ko zama bata yi ba tace taslim zo na aikeki gurin ummi amman karkice nice na aiko ki.


  tace toh anty babba inajinki.


fatima tace dan Allah kije ki tambayo min ummi wai dagaske ne ciki yana fita ta fitsari?


 taslim ta zaro 😳 tace ni wlh bazani ba, kina ganin dazon daga Mubarak yazo gurina ummi tace wai tunda aure nake so nace mishi ya turo, yazun kuma sai naje mata da zancen ciki?


  shiru fatima tayi zuwa cen ta sake cewan dan Allah taslim kije mana.


 Taslim rufe ido tayi tace bafah zani ba, idan kin matsu kitashi muje na raka ki.


  Ba yadda fatima ta iyi Dan haka tace muje.


 suna fitowa haydar ya daure fuska kamar baya dariya sabo da ganin taslim.


 zama sukayi guri daya kamar munafukai kowa bakin shi na motsi.


  ummi ta kallesu tace fatima yaya meya faru?


  shiru tayi kamar bazata yi magana ahankali tace ummi wai ciki yana fita ta fitsari?


  dasauri haydar ya dago ya kalli fatima sannan ya harari taslim


  Cike da mamaki take kallon fatima tace wanne irin  ciki ne kuma yake fita ta fitsari ke waye ya gaya miki?


  haydar ta kalla sannan tace yaya haydar ne yacemin cikin ya fita ta fitsari.

 

 dariya tayi irin tasu ta manya tace wane cikin ne ya fita bayan wanda yake jikin ki, tsokanan ki yakeyi, ta juya barayin haydar tace kaikuma ya zaka dinga firgita ta ai irin wannan sai kasa jininta ya hau



Daure fuska yayi sannan ya kalli taslim yace ke tashi kibar nan gurin.


  Gudu gudu ta mike har tana tuntube ya juya ya kalli ummi yace ummi kisan meye?


   


  🕊🕊

Mmn Yazeed

             🕊🕊🕊

[8:12PM, 5/6/2017] Fadila Lamido: 🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*



97 - 98




Ban sani ba saika fad'a, ummi ke fadin haka cike da haushin haydar.


Dariya yayi sannan yace ummi toh ki sallame fatima sai muyi maganar.


  Tace bazan sallameta ba idan ma bazakayi mgnr ba ka barshi, ta juya gurin fatima tace ke kuma ki kwantar da hankalin ki karya yake miki, cikin ki na nan lfy kalau, kema ban da shashanci irin naki ina kika taba jin ciki ya fita ta fitsari.


  Turo baki tayi tana hararar haydar tana fadin wlh ummi shine yace min wai yanzon haka akeyi.



  Juyawa ummi tayi ta rufe haydar da fada, dan haka ya warware mata kome.


     Bayan ummi ta gama sauraran haydar komawa tayi kan fatima , daga karshe ta koma nasiha tare da lallashin ta da ta kwantar da hankalin ta.


   Hawaye take sharewa, haydar ko ido ya zoba mata.


  zuwa cen ummi tace toh kutashi ku tafi dare nayi.


  Fatima bata tsaya jiran haydar ba gaba tayi , tana tafe yana binta abaya.


  Suna shiga barayin su haydar ya rike fatima, yace


     Wai fushi kk yi dani?


  Rufe idon ta tayi domin ko ganinshi  bata sonyi.


  Saidai azuciyar ta koda taji cikin nanan batajin tsanar shi, saima wani sabon so da takeyiwa cikin, abin da kawai yabata haushi rainin wayon da su haydar suka mata.


  Muryar haydar ce ta katse mata tunanin dayake fadin , fatima banayi haka da niyar yaudararki bane, naga awannan lokacin bani da kalmar da zan rarrashiki da ita ne idan ba wannan ba. amman kema inda kina da wayo zakisan baxan dauke ki da hannu na nakaiki acire miki cikin ba, ni yanzon abin da nakeso dake ki kwantar da hankalin ki, insha Allahu nan bada dadewa ba salis karami zai iso.



  Murmushi ta saki har zuciyar ta taji dade kanta tasa akasa saiga hawaye yana zubo mata.


  Haydar ya kalleta yace toh meye abin kuka kuma, ke babu damar ayi maganar salis saiki kama kuka, kina nufin kin fini sonshi ne?



  Cikin kuka tace ban fika son shiba amman nafika kaunar shi.


nan danan fuskar haydar ta cenza, yace toh naji mubar maganan kawai.


  Shiru tayi zuwacen ta sake cewa kaima wlh idan har zaka fadi gaskiya kasan har son na shima na fika.


   Mikewa yayi cikin daga murya yace nace miki kibar mgnr ko bazakibar ta bane, juyawa yayi har ya fara tafiya ya bude kofar zai fita sai kuma ya dawo idon shi jawur cikin fada yace ai dole ne ki fini sonsa tunda tare aka hayfeku, kuma ni banson kina sonsa ba sai ranar da kika....... kasa karasawa yayi ya dafa kanshi da duk hannuwan shi guda 2 sannan ya girgiza kai ya fita.


   Binshi da kallo tayi itama hawaye ciki da idonta azuciyar ta tace kodai haydar kishi yake da yaya salis idan ba haka ba yaya za,ayi daga mgn sai ya dau zafi haka, mikewa tayi tabi bayan sa ta sameshi adakin shi ya hada kai da gado.



  Karasawa tayi ta dafa shi ko d'agowa beyi ba, tace yaya dan Allah da gaske kk yi sunnan salis zaka saka min idan nahaihu?


  Wani sabon haushi ne ya kamashi domin da ace fatima tasan zafin dayake ji azuciyar shi idan tayi maganar salis da bazatayi ba, badan yanajin kunyan kar ummi tace yana kishi da d'an uwan shiba dasai ya fasa mata baki wata kila daga lokacin zata kiyaye shi, dagowa yayi da jajayen idonshi ya kalli fatima sannan yace


 Ai badan ke zansa sunan ba dan kaina zan saka dan d'an uwa nane tare muka kwanta acikin mahaifiyar mu aka kuma hayfemu tare kuma mukasha nono tare muka girma ,dan haka duk wata kyauna dazaki nuna kina mai a bayan nine, dan ku su ummi da sukai sular zuwan mu duniya bazasu fini kaunar shi ba, bare ke.


  Cikin fatima cike da dariya tace meda wukar, yaya daga wasa saika dauki abu da zafi aini wasa nake maka ni son da nake mishi ma ai dane, Allah ya huci zuciyar ka.


   Fuskar shi adaure yace ke kika sani, fita kibani guri.


   

 Kalon shi fatima tayi damamaki azuciyarta tace wannan wani  irin kishi gareshi dan tunda suka shirya baya taba bari su raba shinfida amman shine yau harda koran ta.


Mikewa tayi da niyar ta fita adakin amman saitaji batason yin hakan saboda tafi kowa sanin halil haydar idai ko har ta fita adakin yau bazaiyi bacci ba wata kila ma sai yayi ciwon ciki, dan haka ta fara kokarin hawa gadon, gefen shi ta kwanta ta daura kanta ajiki shi.


  Ahankali yace wai banace ki fita bane?


Itama daure fuska tayi sannan tace nifa bazan fita ba, kwanciya zanyi, kuma ai nace maka kayi hakuri.


   Baza yayi da ita ya rufe ido dan haka fatima ta zuba hannunta duk 2 cikin rigar shi tana mai cakulkuli tun yana fadin meye haka bari mana, har ya fara dariya, daga karshe ya shiga ramawa.



Tun daga wannan rana suka kara kullewa kamar sa ahad'iye juna sabo da yadda suke nunawa junan su so, tun da fatima ta gane haydar baya son tana mgnr haydar ta daina yi agaban shi, saidai data tuna salis zata shiga daki tai kuka dan son da takeyiwa salis ajininta yake.


  Ayanzun haka dai cikin fatima ya isa hayhuwa girma yayi sosai dan yanzo fatima zama da ker dashima haka, wani zubin idan fatima ta kalli cikin tsoro yake bata, daidai wannan lokacin ne aka tsaida bakin taslim ita da mubarak dane agun kawar ummi , kuma mahaifin shi hamshakin me kudi ne, ba,asa rana me tsayi ba sati 2 kawai akasa


  Fatima bataji dadin saranar da akayi a wannan lokacin ba dako tafiya daker takeyin ta, dan haka lokacin da daddy yake sanar musu ta fara kuka.


 Daddy ne ya lura da ita dan haka yace mamana yayadai?


   Goge hawayen ta fara sannan tace daddy da anbari bayanzun ba, kagani fah bana iya tashi


  Dariya sukayi sannan haydar yace ton idan kina iya tafiyar me zakiyi?


  Bata kulashi ba ta sake cewa daddy dan Allah abari sainan da wata 1.


  Fukar daddy cike da dariya yace mamana ki cire mgnr biki azuciyar ki mu fatan mu Allah ya rabaku lfy, wata kila ma kafin bikin ,kiga kin haihu, ina fatan dai duk kunsaya kayan haihuwa?


   Kan fatima akasa tace nima ban sani ba.


   Daddy ya waiga ya kalli ummi sannan yace kuna nufin ba,asai komai ba har yanzun?


  Murmushi tayi sannan tace alhj komai yana hannu itace dai bata sani  ba.


  yace toh yayi kyau ina fatan dai komai 2 kuka saya?


  ummi ce ta bashi amsa eh , daddy yace to ai yakamata ku nuna mata ko akwai wani abun da take so ba,a saya ba.


   Ummi tace toh mijinta ne yace kar anuna mata.


   Fada daddy ya farawa haydar akan me zaice kar anuna mata, daga karshe yace maza aje anuna mata.


   Dakin ummi suka shiga ummi ce ke nuna wa fatima kayan haydar na zaune agefe.


    Gani tayi komai 2 ake daukowa, daidai da bahon wanka ma guda 2 ne, dan haka tace ummi meyasa naga kayan komai 2?


   Haydar ne yayi sauri yace, sabo da idan wani ya lalace ad'ako wani.


    Harara fatima ta galla mai sannan tace ni bakai nake tambaya ba.


  Ummi ta kallesu tayi murmushi sannan tace fatima haydar boye miki yake, likita yace yan 2 ne acikin ki, dan haka ki kwantar da hankalin ki, insha Allahu lfy lau zaki hayhu.


   Watsi tayi da kayan dake hannun ta tafara kuka.


  Ummi ta bita da kallo nan danan hankalin ta ya tashi ,zuwacen ta mike tayi daki, saboda tsoro amai ta dinga kwarawa, haydar na biye da ita, zuwacen ta rike ciki.


     Hankalin haydar ya tashi, wayar shi ya daga ya kira ummi ya gaya mata halin da fatima ke ciki, ba a dau lokaci ba saigata ta iso.


    Ummi naganin inda fatima keyi tace wa haydar yi maza ka fito da ita muje asibiti.


     Arikece haydar ya wawusu fatima yayo waje da ita





🕊🕊

Maman yazeed

                🕊🕊🕊

[10:01PM, 5/7/2017] Fadila Lamido: 🕊🕊🕊

                    🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

🕊🕊🕊

*_Tsuntsu Me Wayo_*

           🕊🕊🕊🕊🕊



_Storry & written_

              By

        *_Fadeela Lamido_*



    *Na sadaukar da wannan page din ga iyalan 👇marigayi*


    _Alhj Lamido Bello_


   *Godiya ta mussaman ga yan group d'ina Fadila lamido novels ,bansan taya zan nuna farin cikina akan yadda kuke bani goyon baya ba, gasky Ina alfahari daku wannan page din bazai isa nakira sunan ku ba saidai nace Allah ya barmu tare*😍😍


     Jinjina gareku

      

      Faty Afreen

      Cwtjiddah 

        zeezee

     Billy galadanci

       Ummi jafar

   hussaina ubandiya

      zeenasir

    Aisha big girl

    Yar gatan hudah

    Yar mutan yudil

       Hamagee

      Fatima umar abdallah

    Nana zee

 Meenat tabacco

   Anty sa,adatu


  Marubutan👆 mu kenan



 

99 - 100✋




Kai tsaye asibiti suka nufa, daka kalli haydar kasan hankalin shi tashe yake, bayan anshiga da fatima dakin haihuwa ummi ta kalli haidar taga duk jikin shi yayi sanyi, dan haka ta matsa ta dafah shi tace ya haka kaida zaka mata addu,a Allah ya rabasu lfy kuma saikabi ka tada hankalin ka.


    yace ummi ina tausayin fatima sai nake ganin kamar bazata iya hauhuwan yara har guda 2 ba.


   Ummi tace Hmmm haydar kenan in Allah ya yarda lfy zata haihu lokacin dana haifeku nima ai kamar fatima nake .


    Shiru sukayi kowa da abinda yake sakawa.


   Zuwacen ummi tace haydar tashi kaje gida ka karbo min sako gurin taslim.


   tashi yayi badan ransa  yaso ba.


  yana kokarin shiga gidan ummi ta kira wayar shi, cikin sauri ya dauka.


  Muryan ummi yaji cikin fara,a tana fadin Alhamdulillah fatima ta sauka.


   Alhamdulillah ya fara furtawa komawa yayi ya fada mota batare da ya karbi sakon da ummi ta tura shi ya karbo ba.


    Yana isa dakin da fatima take ya nufah ya samu ummi da mama zaune adakin.


  cike da fara,yake kallon su, mama tayi dariya sannan ta mike ta mikamai jaririn dake hannun ta, sannan ta dauko dayan ta sake mikamai , rugume su yayi ya kuresu da ido ganin yaran sunyi kama dashi sosai, idon shi cike da hawaye yace 


   Mama ina hasan din yake?


 Ummi ce ta mike ta taho gurin ta leka fuskar yaran sannan ta nuna mai hassan din tana fadin kaga yadda yaran nan suke kuma haka  kuke sak lokacin da na haife ku, naso ace salis nanan aka haifi yaran nan.


   Nan danan haydar ya fara kuka, daidai lokacin da dada ta fito da fatima daga toilet ahankali take tafiya fukarta kumbure da gani taci kuka ta gaji.


   Ummi ya mikawa yaran ya karasa gurin fatima ya rike mata hannu ahankali cikin rada yace sannu fatima.


  Wani sabon hawayen ne ya sake zubo mata.


  Haydar yasake cewa meyasa kk kuka fatima, keda zaki farin ciki kuma saiki na kuka.


   cikin kuka tace na tuna da yaya salis ne.


   Yace karki damu muyi hakuri kuma ai gawani salis din Allah ya bamu.


   ********


 Washegari suka koma gida cike da farin cike, agidan suka samu yadikko lokacin da haydar yaga yadikko abarayin su daure fuska yayi yace meya kawoki gida na, ko burin kunya kk zoyi.


    Itama daure fuska tayi tace tafiya da fatima nazoyi dan aguri na zatayi wanka.


    Haydar yace wlh baki isaba babu inda zata ina hauka ne zan baki matata ki tafi da ita.


   Dariya sukayi gaba daya dakin.


   Da daddare haydar na xaune adakin ummi saiga anas da mahaifiyar shi sunyi sallama adakin ummi.


 Bayan sun gaisa da ummi anas yazo ya mikawa haydar hannu suka gaisa sannan anas yayi mishi barka


   Kunyace ta kama haydar dan haka ya rike hannun anas sukayo waje, hakuri ya bashi akan abinda yaje har gida ya mishi.


   Anas yace aini daman ban rikeka azuciyata ba, amman abinda ya bani mamaki watannin danaga ka share baka nemeni ba, shine yasani tunanin kodai haryanzon kana kullace danine.


   Dafashi haydar yayi sannan yace baka ba ne , naki zuwa wajen kane saboda ina tunanin indai naje gurin ka zan iya komawa harka da nakeyi ada , wadda bazanso hakan ya kasance ba, dan ni yanzon bana shan komai kuma natsaya ga matata ce kadai, bana bin mata ayanzo.


   Anas yayi murmhshi sannan yace aini ma tuni na daina banayi yanzon bani ma da lokaci yazon tare muke kasuwanci da abban mu duk inda ya saka kafa ina biye dashi, kuma nima ayanzun inada iyali watan na uku da aure.


   Haydar ya zaro ido sannan yadan daki anas yace shine kayi aure baka nemeni ba.


  yace yazan nemeka bayan ka shareni yanzon badan naji lbr nazoba ai bazaka nemeni ba.


  Haka suka cigaba da tattaunawa saigurin karfe 10 suka bargidan.


    Ranara suna ta zagayo yaran sukaci sunan salis da haydar, suna sukayi sosai domin nuna farin cikin so da wadan yaran da Allah ya basu, kowa acikin wannan family daya bude baki cewa yake Allah yama wadan yara albarka.


  Shiko haydar azuciyar shi cewa yake Allah yasa duk su biyo halin salis.


   Itako fatima kirikiri take nuna tafi son salis din dan koda yaushe shi zaka gani ahannuta idan ma nono ne salis din take fara bamawa sannan tabawa haydar.


 Yadikko ce ke zaune da Fatima, ita ke kula da ita.


   Satin fatima 2 da haihuwa akai bikin taslim , zagewa fatima tayi akayi komai da ita dan idan ka kalli Fatima baxakace mejego bace tayi d'as da ita komai nabikin tare akayi da ita kai amarya ne kawai haidar ya hana fatima zuwa.


  Haka zaman su yaci gaba da kasancewa cikin farin ciki da annashuwa gashi  yau kwanan fatima 34 , suna zaune ita da yadikko daki haydar ya kira wayar fatima , bayan ta dau suna gama mgn saita miki ta nufi fita.


   Hajiya tace ina zaki kuma?


    Tace inazuwa hajiya yanzon zan dawo yaya ne yake kira na, bata jira me hajiya zatace ba tayi gaba.


   Hajiya taita zaman jiran dawowan fatima shiru har 12:00pm gashi yaran suntashi sai kuka sukeyi , haka hajiya taita lallashin su amman inna kwana sukayi suna kuka haka hajiya ta kwana babu bacci.


  Da asuba ummi taji kukan su yayi yawa dan haka ta shigo har dakin fatima, samon hajiya tayi tsaye sai faman jijjigasu takeyi .


  Tace hajiya meya same su ina uwar su take.


    Hajiya tace tana gurin mijinta cen ta kwana.


   ummi batace komai ba tamika hannu ta karbi yaran ta wuce barayin ta dasu.


   Sai shidda da rabi na safe ta shigo tana sanye da jallabiyar haydar ta reke kasan da hannun ta saboda ta mata yawa



Hajiya na zaune akasa tana hada kayanta kallonta fatima tayi sosai sannan tace inakwana.


  Amsawa hajiya tayi ba yabo babu  fallasa, fatima ta kalli gadon ,ganin shi tayi babu yaran kuma gashi ta kasa tambayan ta ina yaran suke.


   Zama tayi tai tagumi .


  Zuwacen hajiya ta gama hada kayan ta tamike ta yafah mayafin ta bude kofar zata fita.


  Mikewa fatima tayi tabi bayanta tana fadin hajiya ina zaki?


   Atakaice tace gida zani tunda naga kiyi arba,in harkin koma gurin  miji.


   Bata rai tayi kamar zatai kuka tace bacci ne fah ya kwasheni ban sani ba dan Allah kiyi hakuri, 


  Ko sauraran ta batayi ba ta fita adakin.


 Kukun fatima ne ya fito da haydar yana tambayan ta menene yafaru.


Bayan ta gama gayamai yaja tsaki yace toh ai gwara ta tafi daman ta takuramin.


  Bin bayan hajiya sukayi suka sameta afalon daddy su ummi na bata hakuri tana fadi wlh gida zani bazan zauna ba, yara basu da kunya mezan zauna  nayi.


  Haydar ko ganin inda yadikko take fada sai dariya yakeyi, daddy yakalle shi yace kai fita kaba mutane waje.


   juyawa yayi ya fita fatima ko sai share hawaye takeyi.


   Daddy yamike ya zubawa fatima yaran sannan yace wa hajiya muje na kaiki gida.


  Suna fita fatima ta kalli ummi tace wlh ummi yaya ne yahanani...... 


  Ummi ce ta katse fatima da fadin ni ban tambayeki ba ai mijin kine bakiyi laifi ba, hajiya tana guje miki wahala ne tanason yaranki suyi kwari tukuna.


    Haka fatima ta wuni sukuku saboda damuwar tafiyan hajiya.


  Da daddare ummi ta kira haydar fada tamai akan barin yaran da sukayi gurin gajiya san tace batason ta karajin kukan su dan idan taji kukansu kuma har taga da ganga akabarsu toh fa zata dauke fatima harsai ta yaye yaran Zatw dawo dakin ta.


  Wani sabon amarci suka bude wadda ba,ayishi daba, haydar dakansa yana tunanin wai ya kayi ya zama haka akan fatima ji yake kamar ita kadaice mace aduniya.


  Lokacin nata tafiya yanzo yan biyu watan su 7 kuma a daidai wannan lokacin ne fatima ta fara rashin lfy duk abinda taci saita amayar dashi ta dade tanajin cenji ajikin ta, dan haka yau data wuni amai abin ya dame ta, haydar na dawowa ta tareshi da zance.


   Haydar karame ya dauka yasashi akan ruwan cikin shi sannan yace mekika ce?


   Bakinta cike da miyau tace aikaji abin da nace.


  Haydar ya daga ya daura mata akan ciyarta sannan ya dauki salis ya rugume yace to kodai ciki ne.


   Cikin muryan kuka tace nima abinda nake zargi kenan , dan Allah kazo muje asibiti aciremin.


  Haydar yace kina hauka ne kinga karki sakemin mgnr zubar da ciki kisan dai yanzon ba da bane , idan bakina son ranki ya baci bane karki sakemin wannan maganar.


  Mikewa tayi ta wurga mai haydar , cikin sauri ya saka hannun shi ya  rike shi kuka ya saka saka makon firgita da yayi.


    Fatima ko  waigowa batayi ba , dan haka haydar ya kule.


   Lallashin shi ya shiga yi amman yakiyin shiru, zuwacen salis ma ya fara, haydar ya rasa ya zaiyi dasu, ummi ce taji kukan yayi yawa ta shigo. salis ta gani tsaye ya hada su duk biyun yana jijjigawa.


   Ummi ta mika hannu ya saka mata haydar tace ina mamar su?


  Idonshi jawur yace ummi ki rabu da ita kawai zanje na sawo musu madara.


  Tace akan me wani abune ya faru?


    Cikin fada yace kibarta kawai yariyar nan ta riga ta raina ni kwata kwata bata ganin mutun ci na.


    ummi ta fara kwalawa fatima kira.


  Saigata ta fito sanye da hijjabi , ummi ta bita da kallo tace fatima yazaki bar yara kinaji suna kuka, idan ma wani abu ne ya faru tsakanin ki da haydar aisu babu ruwan su , dan Allah karki kara hucewa akan su, zoki karbe shi kibashi nono.


   Mikewa tayi ta wuce ummi taje gaban haydar tace kawo shi.


   Daure fuska yayi sannan yace bazan bayar ba kije ki fara bawa haydar shine yake kuka.


   Itama cikin fada tace ai yafishi jin yunwa kawai dan dai yana da hukuri ne kabani shi, waccen dama rigimar tsiya gareshi.


   Ummi tace wai meyasa kuke irin wannan ne, ke rabo dashi kizo ki karba haydar din.


   Tana kuka take shayar da haydar karami, haydar ya bita da kallo yace ummi kinga arin abin da fatima takemin ko, wlh banbanci take nunawa atsakanin su wai ita tafison haydar danayi magana saitace wai ai yana da hakuri ne, ummi metake nufi da wannan mgnr Zagina takeyi kenan, ita har yanzun akwai wani abu azuciyar ta, wlh....


  Ummi tace ya isa haka haydar kubar mgnr ni banason fitana ta juya gurin fatima tace waike fatima me yasa kike haka, wadan nan yaran dukka fah yaran ki ne, kefah kikayi yunkuri kk haifesu meye naki na nuna banbanci atsakanin su, kinason su taso da rabowar kaine, yazun kamar wannan dan yaron har kin fara mai shedan rashin hakuri, nasiha ummi ta mata meshiga jikisa

sannan tace tabawa haydar hakuri.


   Ahankali ta fura kayi hakuri.


  Be amsa ba ya juya yace ummi, yanzon ma ciki gareta shiyasa take fushi .


   Zaro ido tayi tace ciki,  toh fah, ai shikenan Allah ya rabasu lfy


   Haydar ne ya amsa da ameen.


    Washegari ummi ta shirya kai fatima asibiti haydar ne kejan motar, bayan sunje suna kan hanyar su ta dawowa Fatima taga wata me gasa masara tace


  Ummi kalli me masara ummi tace zakici ne?


   Tun kafin ta bada amsa  haydar ya tsaya agurin da kanshi ya sauka.


   Zuwacen ya dawo ya mikawa fatima masarar sannan ya shiga motar ya zauna yace ummi kin gane yariyar cen.


   Kallon yariyar tayi cike da mamaki ta bude murfin mutar ta fita,


   Tana zuwa gurin tace ke ina yaron da kk hayfa?.


   Cikin firgici ta mike tace hajiya dan Allah kiyi hakuri wlh daman cen bani da ciki kawai nayi haka ne dan haydar ya aure ni dan allah ki gafar ceni.


   Tsaki ummi taja sannan ta koma motar suka kama hanyar gida.


  Haka rayuwa taci gaba da kasancewa agidan daddy cikin kwanciyar hankali shekaran yan biyu daya suka fara yawo ko ina lokacin fatima cikinta wata shidda,  kuma adaidai wannan lokacin ne taslim ta haifi yarta mece wacce akasawa sunan Aisha, wantan Aisha 4 fatima ta sake haihuwan yan biyu mace da namiji.


   Murna ce ta kama haydar har ya fara cika bakin wai shekara me zuwa yan uku fatima zata haifar mai.


    Alhj yusuf da daddy kuwa ji suke kaamar sunfi kowa farin ciki, bare kuma hajiya yadikko me fatan tara uguwa guda, 


  Ayanzun salis karami yana gun ummi shiko haydar yana gurin mama, dan haka fatima daga ita sai yan biyun ta .


   Ranar da fatima tayi arba,in haydar ya biyo ta har daki da bukatar shi, ke meme taki amincewa domin tsoran karta dau ciki,amman saida haydar yasan yadda yayi ya mata dubara  suka lula.✋


   



    Alhamdulilah


Sai mun hadu a sabon novel din na nagaba


  ~*_Ta mishi illah_*~



 

Maman yazeed


07014197556

🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊



adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *