Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Friday, May 27, 2016

AMINAN***JUNA 101----150

adsense here aminan-juna.jpg

[7:39PM, 5/20/2016] my mtn: AMINNAN JUNA


WHW



Na Xarah~B~B




111-115


koda suka farka daga bacci har ankusa shiga garin katsina da shigar su Katsina baba ilyasu bai tsaya da su ko ina ba sai Lay out, unguwar su Ammi kenan" horn yayi mai gadi ya bude masu gate, parking yayi sa'annan suka fito,

Jin tsayawar mota yasa Futha fitowa da sauri tunanin ko su Amrah ne, kofar shiga parlour suka ci karo "oyoyo mutanan sokoto sannun ku da zuwa" futha ta fada tana mai farin cikin ganin yar uwar ta.

Anan parlour suka tarar da Ammi itama sannu da zuwa ta hau yimasu, bayan sun huta aka wuce dinning suka ci abinci, anan ne Ammi ke tambayar Amrah mutanan sokoto ta ansa mata da "suna lfy ".

Zaune suke su uku adakin Futha suna ta fira, Futha tace " Amrah shin wannan qawar taki bata mgn ne?"murmushi Zarah tayi wanda ya qara fito da zahirin kyanta, Amrah ce ta bata ansa da " Aa tanayi mana me kika gani?" sai a lokacin zarah tace "meyasa kika ce haka Futha?" "Uhm uhm bakomai kawai dai naga bakice komai ba ne tun zuwanku", dariya sukayi sa'annan suka ci gaba da firar su cikin jin dadi da walwala, wayar Futha ce ta dau ruri ganin aunty NABEELERT ce ke kiranta yasa ta dauka cike da farin ciki tace "hello auntyna" banji me akace ba a dayan 6angaren sai naji tace "Allah sun iso tin dazu ma bara na baki amrar ku gaisa kafin mu zo", bayan sun gaisa da Amrah sukayi sallama tare da tsinke wayar.....Urs Zarah~B~B.





116-120


"Haba Farouk meyasa baka jin shawara ne?, yakamata kafi qarfin zuciyar kada ka biye mata ta kai ka gayin nadama a tym din da batada amfani", ajiyar zuciya yayi sa'annan yace "musty kasan fa shi SO baruwan shi da wannan yana zuwa ne a ko ina koda babu son muntun, so baruwanshi da wanda ya dace ko wanda bai dace ayi dashi ba", Musty yace "to naji , amma waya fadama ita ZARAH tana sonka? dahar ka daura wa kanka soyayyar ta haka, haba Farouk ina mai qara baka shawara da kayi hakuri kada kayi sanadin rabuwar way'annan masoya ka tuna fa" AMINNAN JUNA ne" sa'annan........ " Hannun da Farouk ya daga mai yahana shi qarasa mgnr, yace " kaga malam dan Allah ka kyaleni naji da abu daya idan ma zarar bata sona me naka aciki" musty sake da baki yake kallon shi aranshi kuwa ya tausayawa AMRAH dan yasan irin son da takewa Farouk. Baida yanda zayyi da farouk dole ya haqurah ya barshi.


Washegari!!!

Amrah ce zaune akan gado tana tunanin "meyasa Farouk bai kirata ba tun xuwan su katsina?" tin tana hakuri abun har ya fara damunta nd idan ta kirashi wayar bata zuwa, zarah ce ta katse mata tunanin da takeyi tace "my Amrah lfy Kuwa nagan ki haka? Ina kule dake fa duk kin canza tun kafin mu baro sokoto,miye damuwarki haka da har zaki 6oye min ita?"ajiyar zuciya tayi tace "Hmmmm!!! Wlh abun na damuna my zarah tinfa zuwan mu hubby bai kirani ba nd idan na kira bata zuwa, kusan ma ince miki tun kafin mu baro sokoto nake ganin canji a wurinshi, na rasa yanda zanyi dashi, ni damuwa na ma d'aya ne Allah yasa yana lafiya" Zarah tace " amma kuma bana ji kina waya da musty ba jiya?"Amrah tace "ehh wai shima be sani ba ko yana lafiya, munyi dashi zaije ya dubashi a Hostel kin san ya koma can, so kuma shima d'in ina ta nemanshi yaqi picking call d'ina, shi yasa kikaga na damu da yawa" cikin tausayi da jinqan qawarta Zarah tace "kiyi hkr my Amrah may be matsalar network ce, kibari zuwa anjima sai ki qara trying number" haka dai tayi ta bata mgn har ta samu natsuwa.

Shakuwa ce tashiga tsakanin Futha da Zarah kamar sun dade da sanin junan su, ita dai Futha tana jin son zarah aranta nd tana jin dadin zama da ita haka itama zarah take jin son Futha.

"Ammi wai yaushe ne ya AFFAN zai dawo?" ta qarashe maganar cikin shagwa6a, Ammi tace "yakusa dawo insha Allah munyu waya yace baifi kwana biyu ko uku ba ya dawo " Amrah tace "ok Allah ya maidoshi lfy, Ammi kun san fa na dad'e rabona dashi, dan ko a hanya na ganshi ba lallai bane in gane shi nasan shima d'in haka" Ammi tace "injiwa ya fad'a miki? Sai dai idan kexe bazaki ganeshi ba amma shikam dole ya gane ki", ta'be baki Amrah tayi tare da cewa "tou Allah ya dawo dashi lafiya" duka suka amsa da "amin"....... UrsZarah~B~B.



WWA


Fatima~Bello~Bala.
[21/03 10:17 PM] Zara Bb: AMINNAN JUNA



WHW



Na Xarah~B~B




121-125



BAYAN KWANA BIYU!!!

Yaune ranar da ya affan zai dawo daga uk ya kammala karatun shi na likita.

Shirye2 ne suke tayi a gdn na tarban ya affan basu da kammalawa ba sai 12:00pm kasancewar sai 2 jirgin su zai iso,

Sun shirya tsaf kowanan su yayi kyau sosai sai kace wasu yan uku, ammi ce keta zolayar su suna dariya, anan dai suka wace sai airport, da isar su basu jima ba sai ga jirgin ya iso,

Wani kyakkyawan saurayi ne naga ya fito daga jirgin, fari ne tass shekarun shi baxa su wuce 29 ba, ahankali naga ya nufi gurin da su Futha suke tsaye, da gudu Futha taje ta rungume shi "oyoyo ya affan" fuskar shi dauke da murmushi wanda ke qara fito mashi da kyan shi ya ansa mata da "yauwa lil sis".

Rike da hannun ta har suka iso gurin da su ammi suke cike da girmamawa ya gaida mahaifiyar shi, kamar daga sama yaji su Amrah na fadin "sannu da zuwa ya affan" wanda sai a tym din ya gansu ya ansa da "lfy qlw", ahaka suka kama hanyar zuwa gd......Urs Zarah~B~B.





125-130



"Da isar su gd ya affan ya wuce room din shi,bathroom naga ya shiga bai wani jima ba ya fito riqe da towel a hannun shi yana goge ruwan jikin shi, bai wani bata tym ba ya shirya tsaf cikin riga da wando 3Q ya feshe jikin shi da turare yayi kyau sosai, sa'annan ya fito.

A parlour ya same su,"oya tashi muje dinning daman kai kaidai akejira" inji ammi ba musu ya miqe suka wuce dinning, futha ce tayi serving dinsu sa'annan suka fara cin abinci da ka gansu kasan suna cikin jin dadi da walwala "happy family kenan".

Bayan sun kammala parlour suka koma anan fira ta 6arke, shi kuma ya affan sai satar kallon zarah yake yi, kiran sallar la'asar ne ya tada su,dakin su suka wuce don gabatar da sallah, shigar su keda wuya wayar zarah ta dau ruri tana dubawa taga dai wannan sababbiyar number ce da ake damun ta da shi tsaki tayi kana da aje wayar "meyasa bazaki daga ba?" inji futha, nima dai narasa dalilin ta naqin picking din call din nan inji Amrah, kallon ta zarah tayi tace "bakomai kawai dai ban san number bane", Amra tace " bt yakamata ki daga kuda sau daya ne kiji kuma waye ai" Zarah tace "ok naji zan dauka".

Bayan sun kammala sallar ne ya affan ya kira Futha, a dakin shi ta same shi yace "wai lil sis wacece ta tare da Amrah?naga kaman ban santa ba" zarah ce qawar amrah tare suka zo ta bashi ansa, ya akayi ne ya affan?" "no bakomai i just ask kya iya tafiya" tare da bata kayan tsarabar ta harda su amrah sa'annan ta wuce zuwa room dinta.....Urs Zarah~B~B.


NOTE: Plz am very sorry kwana biyu kunji ni shiru bana jin dadin jikina ne shiyasa. Tnx alot. Luv u all my Fans

WHW


Fatima~Bello~Bala.
[7:39PM, 5/20/2016] my mtn: AMINNAN JUNA



Na Xarah~B~B



101-105

" Ummah mun kusa tafiyar "cewar Zarah, Ummah tace "Au daman da gama exam ko hutawa bazakuyi ba sai tafiya?" "Uhm Ummah wane hutu kuma idan muka je ai mayi acan kinsan hutun bawani yawa ne da shiba fa", ummah tace "ehh hakane, yaushe zaku je ne?" " nan da 2 days insha Allah" Zarah ta bata ansa, " ok Allah ya kaimu" cewar Ummah, Zarah ta ansa da "amin Ummah na".

Amrah ce kwance tana waya da Futha sun dade suna waya sa'annan sukayi sallama tare da shaida mata cewa sun kusa zuwa. Ba qaramin farin ciki Futha tayi ba, saboda yanda take tsananun son ganin Amrah, nan suka kashe wayar kowa na mararin d'an uwanshi.

Washegari!!
Ta kama Friday Amrah ce dasu Mum zaune a parlour, Amra tace " Dad jibi ne muke son tafiyar nan xuwa katsina fa" , Dad yace "Au kice har tym yayi kenan ?", "eh Dad yayi" "ok sai ku fara shirye2 kenan, ko dawa wani abune wanda kuke buqata?", Amtah tace " Eh dad ina so zan masu tsaraba ne" Dad yace "ok kamar nawa kike buqata?", sai da tadanyi tunani kafin tace " dad koma nawa ka bayar zasuyi" ,kudi masu yawa Dad ya zaro a aljihu yabata.

Shirye2 sukeyi ba kama hannun yaro sai kace masu Shirin bari kasar baki daya koni Zarah saida suka bani dariya tafiyar da ba wata mai dadewa ba amma sai wannan shiri ake, shiru nayi da bakina na masu fatan sauka lafiya.

Zaune take suna fira da umman ta cikin jin dadi, qarar wayar ta taji tayi saurin dubawa, sunan da tagani yasata daqawa cikin hanzari, "Hello My Amrah ykk?" cewar Zarah dayan bangaran aka ansa da "lfy qlw My Zarah ya umma na?" ta ansa da "lfy qlw take", ok ki gaida ta cewar Amrah" " zataji" "yauwa Zarah na daman inaso ne muje mu ida siyayyar da bamuyi ba saboda time ja qurewa", Zarah tace 'kai my Amrah duk wannan siyayyar da mukayi har sai munyi wata?" "Eh sai anyi ta" qarishe mgnr kamar zatayi kuka, "haba am srry my besty na daina" cewar Zarah "ok to ki shirya gani nan zuwa muje" "sai kin zo amma fa kiyi sauri kafin likacin islamiya yayi", sallama sukayi tare da katse wayar....Urs Zarah~B~B




106-110



Zarah bata 6ata tym ba ta shirya tsaf cikin riga da zane yellow nd wyt atamfa , hijab ma wyt tayi kyau sosai, Amrah na zuwa suka wuce, siyayya sukayi mai yawa sa'annan suka koma gd.

Yau ta kama SUNDAY ranar da su Amrah zasu yi tafiya, Amrah ta shirya tsaf cikin riga da skirt blue nd wyt in colour sun mata kyau sosai ta jawo trollyln ta zuwa parlour, "Au har kin shirya tun da wuri haka?" cewar Mum "eh" Mum, "tou kije kiyi breakfast tunda da sauran lokaci" Amrah tace " uhm mum ni na qoshi", kamar ya kin qoshi me kika ci ne? "bakomai cewar Amrah "oya wuce kiyi breakfast" haka dai tayi breakfast din ba don taso ba,

Har gate Mum da Dad sukayi mata rakiya. "To ilyasu dan Allah ku lallaba Allah ya tsare hanya nasanka baka gudu da mota, tou pls kaci gaba da hakan, sannu bata hana zuwa, saidai a dade ba'ajeba inji hausawa, kabi mota a hankali harku isa, Allah ya kaiku lapia" cewar Dad duka suka ansa da "amin" bayan sunyi sallama, Amrah ta shiga mota suka wuce gdn su Zarah.

Ringing biyu ta daga "dafatar kin shirya?" Cewar Amrah, cikin hanzari Zarah tace "eh na shirya ke kadai nake jira" bata rufe baki ba taga Amrah a gabanta tana mata murmushi, Zarah tace " Au kinma iso shine kika kirani, dariya sukayi gaba dayan su sa'annan Amrah taja trollyln Zarah suka fita,

A parlour suka tarar da ummah, nasiha ta masu sosai tare da masu Allah ya kiyaye hanya sukayi sallama har mota ummah ta masu rakiya sa'annan suka wuce wayar Zarah tahau ruri, koda ta duba taga wannan sababbiyar numbern ne dai da ake damunta, barin wayar tayi har ta tsinke bata dauka ba, Amrah tace "Zarah ki dauka mana ana kiranki kina ji", Zarah tace "rabu dani pls! Wlh an dameni da kira ne da number'n nan, ni bana son disturbing wlh", ta buga uban tsaki, Amrah sake da baki tace "Allah ya baki haquri aunty masifan bani na kashe zomon ba rataya aka bani", Zarah tace "naji dai ki qyale ni..." bata gama fadi ba aka kuma kiranta, switch off dib wayar tayi baki daya tana jin haushin wannan anacen dake kiranta kullun duk da ba dauka take ba, a haka har bacci ya daukesu, saboda tafiya daga Sokoto zuwa katsina ba abune me sauqi ba.........Urs Zarah~B~B.
la
[7:39PM, 5/20/2016] my mtn: AMINNAN JUNA



WISDOM HAUSA WRITERS.




Na Xarah~B~B






131-135



Akwana atashi ba wuya agurin Allah yau su Amrah satin su daya a katsina shakuwa me qarfi ta fara shiga tsakanin zarah da ya AFFAN saboda ta dan fara sakin jikin ta da shi sai dai ba sosai ba, duk da har yanxu bai furta mata yana son ta ba amma su Futha har zolayar ta suke suna cemata matar yaya, tun tana nuna bata so har ta kyale su.

Amrah ce kwance tana ta tunanin abn qaubarta, wayarta ta dau ruri ta sauri ta dauka jin special ring tone data saka mishi, "Haba hubby sai yanxu zaka kirani tun zuwan mu garin nan? Kuma kona kira wayar ka bata shiga", ajiyar zuciya Farouk ya sauke tare da cewa "no my luv bahaka bane wlh", "to yane?" ta fada cikin kunar rai, "banida lfy fa kuma wayana faduwa tayi saida nayi welcome back" ya fada cikin muryar tausayi, "hmmmm!! to meyasa baka kirani koda da wayar musty ce ba? ku bakada number na a kanka ne?" rasa ansar da zai bata yasa yace mata "yanxu dai ba wannan ba plz nd plz am very sorry my luv ki yafe mai kinji" ya fada kamar zaiyi kuka, ajiyar zuciya tayi kana tace "bakomai ya wuce", aranta kuwa wani irin dadi taji daya kirata ga wata soyayyarshi da kullun yake qara mamaye zuciyarta. {Allah sarki soyayya kenan, Allah ya hada mu da masoyan gaskia ba irin su FAROUK ba, ameen ya rabbi},waya suka cigaba dayi kamar batayi fushi da shi ba, ahaka har sukayi sallama tare da tsinke wayar.


Ya AFFAN ne kwance a dakin sa sai juyi yake yi shidai har ga Allah yana son zarah kuma son gaskia yake mata amma ya rasa da yadda zai sanar da ita, ahaka dai har ya yanke shawarar fadawa lil sis dinshi ko zata iya taimaka mashi gurin isar da saqon zuciyar shi,da wannan tunanin har bacci ya dauke shi.

Washegari!!!
Ya affan ne ya kira futha zaune suke suna kallon junan su, ya nisa yace
"lil sis inaso muyi wata mgn dake kinji" Futha tace "ok ina jinka big bro", Affan yace "daman..."sai kuma yayi shiru, dariya Futha tayi don ta gane me yake son fadi tace "daman me ya affan ka fadi mana", "uhm sis kenan Allah ina son zarah amma na rasa ta ina zan fara tun karar ta ne", dariya tayi kana tace " ya affan kenan ai kuwa gara ka fadamata saboda kaga sun kusa tafiya may be ma jibi zasu kuma wlh zarah bata da matsala ina tunanin zata amince dakai".....Urs Zarah~B~B.





136-140



" Ido ya zare da gaske kike lil sis"? Tace "Allah da gaske nake ya affan gara ma ka fadamata", Affan yace "to yanxu ya kike ganin za'ayi?" Sai data murmusa sannan tace " Kawai kabari na turo ma ita yanxu dana shiga ciki, amma dan Allah karka kopsa big bruhh" yace "ok sis tnx alot, bazan kopsa miki ba".

Da shigar ta dakin da fara arta ta kalle zarah tace "my cwt Zarah ya affan na kiran ki yana parlour" ido ta xare tace " ni? Ya Affan?" "eh ke fa" Futha ta fada tare da neman wurin zama ta zauna.
A parlourn kuwa ta same shi yana zaune kan kujera a kasa ta zauna "ya affan ina wuni" ta fada cikin girmamawa ya amsa da "lfy qlw ya baqunta?" " Lafiya qlw" tace atakaice, yauwa zarah daman ina... sai kuma yayi shiru ganin shirun yayi yawa yasa yace "yaushe zaku wuce ne?"
Jibi insha Allah ta bashi ansa ok Allah ya kaimu ta ansa da "amin" zaki iya wuce wa, "ok"

Bayan ta wuce kuma duk yaji haushin abunda yayi why why nakasa fadamata,

Zarah ce kwance tana waya da umman ta sun jima suna waya kana sukayi sallama.Alamar shiguwar text taji ganin number ya affan ne yasa ta budewa da sauri ta fara karantawa kamar haka:

"I want to treat you lyk a queen simply bcos you rule my world. I am at ur Service, ur majesty". I really really love u, i hope u luv me too.

Ajiyar zuciya tayi kana ta aza wayar kan kirjin ta, koh dama shine ya affan ke son fadaman ranar da ya kirani? haka ta cigaba da tmbyr kanta, shigowar su Amrah ne yasa ta natsu bt still ta juya mgnr "i really really love u, i hope u luv me too" mgnr Futha ta dawo da ita, wai mekike tunani ne haka inji Amrah, uhm bakomai ta bata ansa..... Urs Zarah~B~B




WWA





WISDOM HAUSA WRITERS

Fatima~Bello~Bala.
[23/03 11:40 PM] Zarah B B: AMINAN JUNA

WISDOM HAUSA WRITERS.


Na Xarah B B

141-145

A daren ranar haka Zarah ta kwana da tunanin Affan, amma kuma ta kasa mishi reply da ta amince, a bangarenshi shima tunanin shi bai wuce qila Zarah bata karbi soyayyarshi ba, haka ya kwana kamar wani zautacce dan son da yakewa Zarah bai misaltuwa, dis is his first time daya fara soyayya, shi yasa yake jinta a jinin jikinshi.

Washe gari tunda safe Zarah ta tashi kamar yanda ya saba ta shiga kitchen, bata tsaya jiran su Futa da Amrah ba ta hau hada masu breakfast n haka Zarah take bata da ganda ko kadan, komai yawan aiki ita baya bata haushi.

Bayan ta gama ta jera komai akan dining table ta shiga ta kira kowa kamar yanda ta saba amma sai ta samu kanta da kasa kira Affan, har sun zauna mum tace "wai ina Affan ne? Hala nawar tashi ce daya saba? Dan na tavvatarda Zarah ta fada mashi tunda kullun saita fada mashi", Zarah sai qwalo ido take sai ji tayi ance "kamar kin sani kuwa mum, ta riga fada min akan kowa, na tsaya yin wanka ne", kyakkywar ajiyar zuciya Zarah ta sauke tare da sinne kanta qasa, koda suka hada ido ya qifta mata qwara daya har cikin ranta taji, taga kuma zahirin soyayyarta a idon Affan, da wannan tunanin suka kammala kalaci itakam kadan taci bada yawa ba.




146-150



Bayan sun gama komai na gida Futha tace "yau muke resuming a skul fa kuma ya kamata inje, kunga saiku takani muje tare daga nan har kuga yanda skul din mu take", Amrah tace "aikam haka ya dace, sai mu dora girki da wuri yanda zamu gama da wuri", Futha tace "ai da yake ma yau baba Rabi zata dawo, nasan da wuri zata zo", Amrah tace "hakane kuma, wai qawa yau ya akayine kikayi shiru?" Budar bakin futha cikin sauri tace "she is in love fa" suka dauki shewa harda tafawa, zarah dai batace masu komai ba dan tasan gaskiya suka fad'a, sai can kuma tace "ai qawa da yake kin samu baki dole kimun iskancin da kikeso, dan kin samu Farouk ya kiraki ne fa", wayar Amrah ta dauki ruri da farin ciki tace "kinga dan halak, bawan Allah ana cikin gulmarshi sai gashi ya kira, wama yasan ko jikinshi ne ya bashi", daukan kiran tayi tace "hubby how fa?" Bai bata ansa ba sai yace "dear pls idan kina kusa da Zarah ki bata, ina son gaisawa da ita", cikin kishi Amrah tace "shine kuma bazaka karva gaisuwata ba ko", haquri ya bata nan da nan ta haqura saboda bata sin laifinshi, ta miqawa Zarah wayar, Zarah tace "lapia?" Amrah ta mayar mata da "I dont know, just take d phone kedai zaku gaisa ne I thinks", kar'bar wayar tayi tace "na Amrah ya kake?" Sai daya sauke ajiyar xuciya alaman missing d'inta tukuna yace "lafiya kalao, wai me yasa baki damu dani bane Zarah? Me yasa bazaki dauke ni kamar yanda Amrah ta daukeni ba?" Mamaki sosai maganarshi ta bata tace "ban gane ba", saurin kawar da maganar yayi yace "barshi kawai dear, xan kiraki anjima amma pls karki daga kiran a gaban Amrah", "tou" kawai tace tare da miqawa Amrah wayarya, koda ta kara a kunne taji har ya kashe, abn ya bata haushi sosai amma sai ta kawar dan bata so qawarta ta fahimci tana kishinta ne.

WISDOM HAUSA WRITERS.

Fatima Bello Bala adsense 2 here
Share:

2 comments:

  1. Mugu zai shiga tsakanin aminai

    ReplyDelete
  2. Kai wannan badan xamfarabane

    ReplyDelete

please after reading drop down your comment here!...

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *