Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Thursday, February 2, 2017

Alkawari complete

adsense here

[10:55PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: ★ALKAWARI★ . Part 1. Yunkuri nayi domin intashi amman naji gaba daya nakasa yin komai sakamakon rashin karfin jikina, wani zafi naji a hannuna kamar antsiramin wani abu cikin hanzari nayi sauri na dagashi, sai lokachin nalura da wata allura soke ga hannu na dawata roba doguwa, nanne nabi robar dakallo har inda tushenta yake, abinda idanuwa na suka gani shine yadauremin kai tare da bani mamaki. Ledar jini che nagani arataye, yana biyowa tachikin wannan roba mai allura yana shiga achikin jikina. A chikin zuchiyata nake tambayar kaina, mike faruwa ne har ake karamin jini? Nanne nakali kane na wanda yaketa murna yana faman danna wayarsa domin yakira umma na yafada mata na farka amman ntwrk ya hanashi, kunsan network din 9ja da matsala... nache ahmad meyafaru dani ne akemin karin jini, budar bakinshi sai yache "yaya yusuf awarka ashirin da hudu kwanche anan, wannan itache leda ta ukku da akasanya maka" rufe bakinshi ne yayi dai dai da turo kofa da akayi,.... wani mutum ne mai matsaikachin tsayi da alama shine likitan dayake kula dani saboda ganin yadda yayi shiga ta fararen kaya kamar wata sabuwar gawa. ba tareda wani bata lokachi ba ya karaso a'inda nake kwanche, tare da tambayar kanena chewa, tunyaushe yafarka? sai yachemai "yanxu yafarka bada dadewa ba", a nanne naga yabuda wani file dake hannunsa yana karantawa tachikin siririn farin gilashin dake sargafe a idanuwansa, batare da ya sakeyin magana ba yabude kofa yafiche abinsa. Jim kadan sai gashi yadawo da magunguna achikin leda, yaba kanena tare da umurtarshi yadda zaya bani maganin. Ananne ya yafiddo yabuda yabani wasu kwayoyi tareda ruwa achikin cup domin insha, amman achikin raina inata kokonto wane asibiti ne wannan masu bada magani kyauta batare da masu jinya sunbiya kudi ba? Ina gama shan maganin, najuya domin ajiye kofin akan wani dan teburi dake gefen gadon da nike kwanche, ananne naga wata yar dunkulalliyar takarda wadda ake kimlache sako mai mahimmanchi achikinta, wadda ake kira da "envelop", nadauka tareda kokarin duba ko minene achiki. sunan yasmeen ne nagani abayan takardai wannan ne yasa na kagu da inbude domin ganin abinda ke kunshe achiki, ina budawa sai naga wata yar takarda mai dan tsawo ta fado daga chikin envelop din, chikin hanzari nasanya hannu nadauka tareda duba abinda ke achiki, wanda idanuwa na suka bani tabbachin chek ne nabanki, mai dauke da kudi naira naira dubu dari biyar, 500,000naira a rubuche, tare da sa hannun yasmeen,... Nanne naji wani irin faduwar gaba, kasanchewar ni bako ne awurin kama kudi masu wannan irin yawa haka, lokachi guda kuma xuchiya ta tambayeni me yasmeen take nufi da wa'annan kudin masu yawa? Idan kyautache tayiman, to miye silar yiman wannan kyautar haka? Ananne namaida hankali na akan envelop sakamakon akwai wata takarda wadda banfiddo ba, hannu na nasanya achikin emvelop din tare da zaro wata takarda wadda take chike makil da rubutu, kamar haka.... [10:56PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: Alkawari Part2 Nafara karantawa kamar haka.... "amincin Allah ya tabbata agareka masoyina tauraro acikin taurari, nasan zakayi mamakin abnda nake kokarin sanar dakai sakamakon alkawarin damukayi na zama dajuna har abada, yusuf kasan inasonka kuma na tsani dukwani abnda yake kokarin shiga a tsakaninmu, shiyasa xuchiyata take takaichi tare da tsoron sanar dakai saura kwana biyu jirginmu zai tashi ranar asabar, sbd abbana ya matsa akan dole sai nafita waje nayi karatu, nayi iya kokarina domin inkauda wannan maganar amman abin yachi tura, shiyasa ma haryaje yachi gaba da shirye shirye batareda ya sanar dani komai ba, saida lokachi yakure sannan yafadamin ya samarmin admission, inshirya domin tafiya "massachusett (code fish) university" dake london... yusuf dan Allah karikemin soyayyata amana zandawo bayan nagama karatuna kuma kai kadaine namijinda xuchiyata takeso amatsayin abokin zaman rayuwa, kuma ga kudinan kaje bank ka amsa domin duba lafiyarka... Daga mai kaunarka "yasmeen jafar muhammad"... Bayan nagama karanta takardai wasu hawaye sukarinka yin ambaliya suna sulalowa ahankali sunabi tabisa kumatuna, wani sashen xuchiyata kuma yana fadamin "wannan ba abin tada hankali bane, abinda zakuji dadi ne saboda neman ilmi tatafi kuma zata dawo" wani bangaren nadaga xuchiyata kuma yanata tinanin yadda rayuwata zata kasanche batareda yasmeen ba"... Karar bude kofa naji wanda shine yayi silar fiddoni daga tekun tinaninda na afka, tunkafin sushigo naji sunyi sallama, muryar mahaifiyata che naji tareda kanwa ta suna shigowa, Karasowa tayi agabana tareda yin magana dawani irin launi mai nuna alamar tausayi karara "yaya yusuf ya jiki" na amsa jiki dasauki kanwata, sai alokachin mahaifiyata ta ida karasowa a'inda nake tareda fadar "sannu dannan kaji ya jikin naka"?? Nikuma sai nafada "da sauki umma" a takaiche... Lokachinne takalli ahmad dake tsaye abakin gadon ya sanyamu agaba da alama tinanin wani abu yakeyi, umma che takatse shi daga tinanin dayakeyi, "ahmad me likitan yafada ne akansa?"ahmad yadago kansa tareda ba umma amsar tambayar datayimasa "yaji sauki sosai umma, kuma doctor yace idan wannan ledar jinin takare za'a iya sallamarshi gobe in Allah ya yadda" bakaramin dadi naji ba danaji ahmad yafada gobe za'a sallameni "nasan zankara ganin yasmeen" abnda nafada kenan achikin xuciyata batareda kowa yajiba... Shiru kowa yayi wurin seconds talatin sannan najuya nakalli kanwata tana tayin wasa da yan yatsun hannunta, sannan nakatse shirun da tambayarta, kanwata yau wace rana? " yaya yusuf yau juma'ah (friday)" atakaiche tafadaman tana kallona da alamar mamaki karara a fuskarta na ganin yanda namanta lissafin kwanaki, nikam bandamu da abnda take nufiba saima wani dadi danakeji achikin raina ina fada gobe asabar in Allah ya yadda kafin su yasmeen su tafi za'a sallameni.... Haka nawuni tunani tareda kosawa gobe tazo, ji nake kamar injuya agogo kawai kowa yaga lokachi yakoma karfe 6 nasafe, wanda danasan abinda zai biyo baya, da banyi zumudin zuwa filin jirgi ba da niyar yima yasmeen bankwana...... [10:59PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: Alkawari Part3 A daren ranar juma'ah bawani bacci nayiba sosai wanda zai ishi idanuwana saboda rigimar danarinka yi da bacci akan bazanyiba shikuma yazo yayiman kane-kane a idanuwa, nikuma gani nake idan nakwanta lokaci bazaiyi gudu ba sosai, nafiso inayi ina duba agogo, shiyasa duk bayan dakika daya ko biyu sai nadaga kaina naduba agogon dake makale ajikin bangon asibitin, haka nakasance bankwanta ba sai wurin karfe 02:30am na dare sakamakon karfina da bacci yaci, shima hakan yanada nasaba ne da ruwan da aka tafka jiya da daddare achikin garin namu na katsina wani sanyi yarinka shigowa tako ina har saida nasanya mayafi na lullube, ina lullubewa shikuma bacci sai yasamu wurin zama a idanuwa na....... Cikin ikon Allah batare da wani bata lokaci ba, gari na wayewa saiga likita yazo yaduba lafiyata tareda bada iznin zamu iya tafiya gida yanxu saboda ansamu abinda akeso, dadi da murna aguna abin ba'a magana, tamkar wanda akaba kyautar kujerar makka domin sauke farali. Bayan fitar likita sai kuma ga mahaifiyata tazo itada hadiza domin kawomana karin kumallo, ananne ahmad yashaida masu ansallamemu. Shiryawa mukayi muka tattara komai namu domin tafiya gda, fitowa mukayi daga asibitin muka doshi tudun wada..... bayan munxo gda ne nashirya domin infita batareda kowa yasani ba, sbd idan umma tasan zanfita, bazata barni ba... Tsohon mashin dina najawo wanda idan ina tafiya kararshi tamkar ana bakacen tsakuwa acikinsa, ina sauri intafi saboda lokacin tashin jirgin yakusa saura 30 minute, bantsaya ko inaba sai filin jirgi, na'aje mashin dina inda aka tanada domin ajiyar ababen hawa.... Wani irin faduwar gaba naji saboda abinda idanuwa na suka hango... Wata mace ce, wadda nikeda tabbacin aunty bilki ce...... Aunty bilki mace ce mai matukar masifa kuma ta tsani talaka batason talaka ko kadan, kanwa ce ga alhaji jafar muhammad mahaifin yasmeen, wanda babban dan siyasa ne wanda yarike mukamai daban daban acikin mulkin nigeria, matarsa guda daya kuma yanada 'ya 'ya guda ukku, biyu maza sai daya mace, usman, aliyu sai yasmeen yar autarsu.... Aunty bilki ta taba yin aure wanda ta auri "ibrahim sabo", abokine ga alhaji jafar, amman saboda tsabar masifar aunty bilki, dole tasa suka rabu da mijin nata tadawo gidan yayanta da zama tareda da danta guda daya wanda take masifar so kuma take nuna masa gata, wanda suke kira da "Abba".........Bayan natsaya ina tinanin tayadda zantunkari aunty bilki, nasan idan taganni bazata barni inshiga agun yasmeen ba, wani bangaren na zuciyata kuma yache "kaje kawai babu abinda zaifaru" cikin karfin hali naci gaba da tafiya, ina karasawa agunsu, sai naduka nagaida ta, wani irin kallo tayiman tareda yatsine fuska kamar taga wani mummunan abu, cikin bacin rai take magana "kai maye har anan saida kabiyota? Wai kai wane irin dabba ne? Yasmeen tayi kama da kalarka ne? banza matsiyaci talaka wanda rayuwarsa batada wani amfani", nidai bance komaiba, kawai na sunkuyar dakaina ina sauraren ikon Allah... Abayan aunty bilki kuwa wasu bakaken mutane ne katti guda biyu masu jajayen idanuwa, tsaye suke kikam ko motsawa basuyi kamar gumaka, batareda tayimasu wata magana ba, kawai tadan juya kanta kadan, kamar tana kallon kafafuwan mutanenda dake bayanta, cikin kwarewa da sanin aiki irinnasu, har suka gane abinda take nufi, cikin zafin nama sukayo kaina suka sungume ni inata billayi, sukanufi wani dan jeji dani sukayiman bugun tsiya kamar zasu fiddamin rai, saida sukaga nadaina motsi sannan suka kyaleni, daman ba cikakkar lafiya gareni ba, anan nasuma sukuma suka kama hanya sukayi tafiyarsu.... Bayan wani dogon lokaci sai nafarka, ganin yanda yanayin garin yachanza nayi zaton yamma ce tayi, amman azahari dana duba agogo sai naga karfe 01:30pm ananne sai nagane hadari ne yamaida garin haka kamar za'ayi ruwa..... Dakyar nasamu nafiddo kaina bakin titi inazuwa nan naji kamar ana juya duniyar gaba daya komai yakoma upside down anan nakara faduwa, daganan bansan abinda yakara faruwaba saidai kawai nabude idona naganni acikin asibiti, daga gefena kuma wata kyakkyawar yarinyace nagani matashiya da gashinta dogo har gadon baya, "achikin raina nace ita tahuta basai tayi acuci maza ba" ina dago kaina nahada ido da ita, kyakkyawa ce ta bugawa a jarida, ga idanuwanta dara-dara, fuskarta tana dauke da wani dan siririn hanci kamar biro, wani irin murmushi tayi wanda yabayyana fararen hakoranta tareda fadar "sannu" acikin wata siririyar murya mai zaki kamar ana busa sarewa.. [11:00PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: Alkawari Part4 Cikin tsoro nake tambayarta "a'ina ne kuka kawoni?" "ku suwaye" cikin sanyayyar murya naji tana fadar " kwantar da hankalinka bamuda niyar zaluntarka" wata ajiyar zuciya nayi wadda take nuna alamar hankalina ya sauka daga kololuwar tashinda yayi, sannan ta tashi tafice abinta batareda takara yin wata magana ba... Wani mutun ne yashigo dakinda nike dawasu karikitai a hannunsa irin wa'anda likitoci sukeyin gwaje gwaje , tareda ledar magunguna, turo kofarda yayi ne yabani damar ganin abinda ke wajen dakin, sai alokacin nagane ashe ba'acikin asibiti nake ba... Karasowa yayi agabana yaci gaba da sanyaman magani a wurarenda naji raunika ajikina, bayan yagama, sannan yabi jikina yanade da bandeji, lokacinda yagama aikinsa shine yayi dai dai da dawowar wannan matashiyar yarinyar wadda bansan ko wacece ba. Zama tayi akan wata kujera wadda take a gefen gadon danake kwance sannan tafara magana dacewa "bawan Allah inaso kafadamin ko kai waye kuma suwanene sukayimaka wannan aikin? wani dogon lumfashi naja sannan nabata labarin abnda yafaru dani a filin jirgi tundaga farko har karshe.... Bayan nagama ne sannan nakara da tambayarta, ita wacece kuma a'ina kuka kawoni?... Sunana haleematu "Badole bane kasan ko ni wacece" tafada ayayinda take girgiza kanta, "amman inaso kayadda dani, kuma kasanya aranka na taimakeka ne kawai kuma banida wata manufa bayan hakan, kuma nan dakake gani gidan gona ne. "nakawoka nanne, sbd bansan ko suwaye sukayimaka wannan abinba shiyasa naji tsoron shiga dakai cikin gari....... Yau kwana biyu kenan rabona da gida, hankalin kowa ya tashi bama yan gidanmu ba kadai, hatta mutanen unguwarmu suna chikin damuwa, anyi sanarwar gidajen radio da t.v amman babu wata magana mai dadi... Tafiya muke achikin mota bamutsaya ko inaba sai acikin garin daura...... Zaune suke acikin wani makeken fallow tsararre wanda yake daukeda abubuwan kayatarwa dayawa, Alhaji usman ne zaune shida matarsa hajiya binta, sun maida hankalinsu akan makekeyar t.v din dake makale ajikin bango. "alhaji kaidai bakada wani channel din kallo sai kttv" matarsa ce tafada ta fuskar tsokana, "hajiya kenan ai kallon kttv yanada amfani saboda kana gida zakasan halinda garinku yake chiki dama kasarku baki daya... Shigowarmu a falon ne yayi silar tsaidasu daga firar dasukeyi tareda maido kallonsu akan kofa domin ganin wa'anda ke sallama. Barka daxuwa diyata yar auta daga ke babu wata duk mai sonki shine nawa makiyinki ko kallo bai isheni ba" hajiya binta che takeyiwa diyarta wannan kirarin. Alhaji yadubeni tareda bani umarnin inzauna, bayan nagama gaishesu ne sannan alhaji yake tambayarta wanene wannan ko abokin karatunki ne? Wani murmushi tayima mahaifin nata tareda fadar "a'a dady", sannan ta sunkuyar dakanta tagayamasu duk abnda yafaru, alhaji usman yanuna tausayi karara a fuskarsa..... Alhaji usman salisu zango mahaifin haleematu ne, kuma haifaffen garin daura ne dan asalin garin zango, babban dankasuwa ne wanda yayi suna acikin garin katsina, matarshi daya Itace hajiya binta da diyarsu guda daya haleematu......Muna nan zaune sai mukaji ana sanarwa a cikin t.v... Kowa tsuru-tsuru yayi babu wanda yayi wata magana saidai kallonda Alhaji yakeyiman kamar mai niyar gano wani abu acikin fuskata. Nikau hankalina yayi matukar tashi domin jin yanda ake nemana kamar kudi, sai alokacin tunani na gaba daya yakoma akan gida, cikin kaguwa da rawar jiki namike tareda yimasu sallama daniyar tafiya gidanmu saboda nasan hankalin kowa a tashe yake yanzu sakamakon rashin ganina... Cikin sauri nanufi hanyar fita waje, muryar Alhaji usman ce ta ratsa kunnena "yaza'ai katafi kai kadai batare da wani ba? Kaduba fa kaga yadda jikinka yake, yakamata ko wanka kayi kafin katafi ko, yakarasa maganarsa da yanayin tausayi karara a fuskarsa. A ranar nagane gidan "Alhaji usman salisu zango" gida ne na mutunci kuma sunsan darajar mutane. Bayan nagama komai nayi shirin tafiya, kamar wani dansu wanda suka haifa ne zaya tafi, haka sukazo mukayi bankwana, nayimasu godiya sosai akan taimakonda dasukayiman... Haleematu ce nagani tsaye a gaban mota tanajiran inxo mutafi, har ta tada mota sai ga hajiya tafito dasauri tana kiran sunanta, chikin sauri haleematu tafito daga mota tanufi wurin mahaifiyarta domin taji kiran me takeyimata, bayan sundan tsaya suna magana wurin minti daya, nidai bansan abinda sukeyi ba, saida suka gama sannan hajiya tashige gida haleematu kuma tayo guna fuskarta da alamar damuwa, tace " kayi hakuri yanxu dreba zaizo yakaika gida, ni bazansamu damar kaika ba sbd wasu dalilai" nidai ban nuna mata naji komaiba, amman acikin zuciyata ina tambayar kaina "meyasa tafasa kaini dakanta"... Tsayawa nayi agabanta inayimata godiya akan abin alkhairinda tayiman, murmushi kawai tayi tareda cewa " babu komai na taimake kane saboda Allah bani bukatar wata godiya daga gareka, nima wata rana zan iya zuwa agunka domin neman taimako" haba haleematu ni ai banida wani abu wanda zaki nema aguna. "hmm hausawa fa sunce ba'a san inda rana ke faduwa ba" tafada lokacinda daidai lokacinda idanuwa na suka shiga acikin nata...... [11:02PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: Alkawari 5Part5.... babu komai na taimake kane saboda Allah bani bukatar wata godiya daga gareka, nima wata rana zan iya zuwa agunka domin neman taimako". haba haleematu ni ai banida wani abu wanda zaki nema aguna. Na kare maganta tareda yimata kallo wanda yake nuna alamar mamaki "hmm hausawa fa sunce ba'a san inda rana ke faduwa ba" haleematu tafada tana kallona... inkau har akwai abinda zaki nema aguna to na tabbata dakin nema nikuma zanyimaki koma minene.... Ahaka dai mukayi bankwana, sannan tajuya fuskarta ixuwa inda wasu mutane da suke zaune, da alama yan aikin gidan ne, sannan takira " sadam! Sadam!!" har sau biyu, sannan naji wani ya amsa "na am hajiya" tache kakai wannan mutumen a katsina "angama hajiya" yafada atakaiche... Daganan muka dauki hanya muka doshi garin katsina... Bamu zame ko inaba sai unguwar tudun wada, sadam dreba ya saukeni adai dai kofar gidanmu sannan yakada motarsa tareda kugamata wuta.... Ina shiga gida khadija ce nagani aduke tana hura wuta, sallamar danayi ne yasanya ta dago kanta. Da gudu ta nufoni tayi tsalle tafada ajikina tareda fadar yaya yaya, hawayenda suka zubo daga idanuwanta ne suka hanata fadar wata magana, saidai murmushi kawai takeyi wanda bayada maraba da dariya, sai alokacin nagane hawayen murna ne takeyi.. Khadija kanwata ce itace yar auta a gidanmu, mu ukku ne mahaifinmu ya rasu yabari, ni sai ahmad sannan khadija. Jin muryata ne yasanya mahaifiyata fitowa daga daki cikin murna muna hada ido da ita, kawai sai naga ta duka ta daga hannuwa sama tanayima Allah godiya da yamaido mata danta. Bayan nazauna ne umma tanemi tasan abinda yafaru dani, nikuma nakwashe komai nafada mata tundaga farko har karshe... Bayan nagama ne nake tambayarsu ina ahmad?? Sallamar da akayi itace ta hana su umma bani amsar tambayar danayimasu... Wani dan saurayi ne yashigo tareda tambayar "anan ne gidan su ahmad bashir muhammad? Nace eh nanne, kafin inkara wata magana, sai naji yakuma cewa "ana bukatar ganinku da gaggawa saboda yanxu haka yana emergency a general hospital sakamakon mota data kadeshi" nan take muka dunguma xuwa asibiti. Dukda bawani nisa kedakwai ba daga unguwar tamu xuwa asibitin ba amman saida mukahau mota kirar (keke napep), wadda kanawa suke kira da (adaidaita sahu). Shigarmu keda wuya muka dauki hanyar da zata sadamu da emergency, muna shiga muka nufi dakinda ake kai yan accident, wani likita yataso yatarbi gabanmu tareda fadar muyi hakuri yanxu ana chikin dubashi idan angama za'a yimaku magana, yanuna mana wasu kujeru dake jere ajikin bango, muka zauna... Jim kadan saiga wani dan tsamurmurin likita yafito mai wani katon kai, fuskarshi da alamar damuwa karara kamar wanda yake shirin yin kuka, cikin hanzari natashi nakarasa agunshi tareda tambayarshi likita ya jikin nashi?? Sunkuyar dakai yayi daga bisani kuma sai yadago kansa tareda fadar..... [11:04PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: Alkawari 6-7Part6...... Dago fuskarsa yayi, wadda tuni hawaye sunyimata kawanya sannan yakara dacewa, "munyi iyakacin kokarinmu naganin mun ceci rayuwar wannan bawan Allah, amman babu yadda zamuyi Allah yariga ya yanke hukunci, saidai kawai aci gaba dayimasa addu'a Allah yajikansa kuma ya gafartamai!!!" yana gama fadin maganarsa kawai yawuce gaba batareda yatsaya yin wani abuba, Umma dake tsaye a gefenmu babu abinda ke fita daga bakinta sai "Inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un"yayinda khadija kau kuka kawai take rusawa abinta batama ko tinanin acikin mutane take..... Koda yaushe umma acikin tinanin rashin ahmad take, munyimata magana wannan tinanin zai iya haifar mata da matsala, amman taki saurarenmu sai abinda yayi gaba. Bayan rasuwar ahmad da sati daya, inacikin daki sai naji karar khadija, cikin sauri nafito domin inga abnda ke faruwa. Umma ce nagani kwance abakin kofa dasauri nakarasa na tambayi khadija lfy miya faru? Bantsaya jin amsa daga garetaba kawai nafita waje dasauri nasamo mota bamu zame ko inaba sai asibiti... Batare da bata lokaci ba akashiga da ita domin duba lfyarta.... Mundauki kamar awa guda (1hour) zaune sai wata likita mace tafito, cikin hanzari natashi na tarbeta tunkafin takaraso nake tambayarta doctor tana ina? Dagamin hannu tayi tana magana ahankali, "ku kwantar da hankalinku munyi iya gwaje gwajenda zamuyi mungano cewa jininta ne ya hau, saidai kuma faduwar datayi tasamu matsala a kashin bayanta..." tanagama magana sai na tambayeta, likita yanxu miye abin yi? Batareda tabani amsa ba, sai dai ta nunamin wani office tace inshiga likitan da zaiyimata aiki yana nan ciki, Shiga nayi da sallama sannan nazauna akan daya daga cikin kujerun da aka tanada domin masu ganin likita... Zaune yake hankalinshi kwance, ya dukar da kanshi a kasa yanata wasu yan rubuce rubuce, daga bisani kuma yadago kanshi "kune wa anda kukawo wannan matar?" yakarasa tambayarsa yana kallona ta cikin siririn farin gilashin dake sanye a fuskarsa. Gyada kai nayi kamar kadangare cikin wata sarkakkar murya nabashi amsa "eh nine" atakaice... Sannan yace marar lafiyar tana bukatar aiki sakamakon faduwa datayi akan wani abu wanda yayi silar fitar wani kashi daga cikin kasusuwan bayanta, kuma kashin da yafita bai tsaya a'inda yakeba, ya bar wurinsa yafada akan (spinal code) wanda hakanne yasanya bata iya yin komai dakanta, tundaga kugunta har zuwa kafafuwanta sundaina aiki, bazata iya yin komaiba, kuma kome zakayimata bazatasan kanayi ba, daga kugunta xuwa abinda yayi samnta har kanta nanne kawai zaka taba taasan kataba. kuma bakomai bane yasanya haka sai wannan kashin daya je agun (spinal code) din yayi kane kane. Yanxu dole sai anyimata aiki, kuma ana bukatar kudi (naira dubu dari da ashirin) kuma tana bukatar aiki da gaggawa sbd kashin yanada tsini, idan ba'ayi aiki da gaggawa ba zai iya yin silar datsewar (spinal code) din, kuma idan tadatse babu maganar gyarawa saidai hukuncin Allah. Nan take zufa tayoman lale marhaban, duk ta mamaye jikina kamar wanda aka tsamo daga cikin teku, tinani na kawai ina zansamo wa'annan kudin, nan take natuna da chek dinda yasmeen tabani lokacinda zata tafi makaranta, cikin azama da kwarin guiwa na nufi gida, ina shiga na nufi dakina, wanda yakoma kamar dakinda mahaukata ke kwana, kana shiga wasu ledoji ne bakake da farare, zasu rinka yimaka barka daxuwa, daga gefen hannun dama kuma wasu kujeru ne murgudaddu wa'anda suke shirin burmawa da duk wanda yazaunasu batareda ixni ba, gefen haggu kuma wani teburi ne wanda yake kama da teburin masu shayi, a samanshi wata tsohuwar t.v ce black and white wadda nima bansan shekarunta ba, daga kasa kuma wata shekararriyar radio ce wadda marhin gidan kaset dinta ya dade da tafiya yawon duniya, daga ganin radion zaka fahimci ita kanta ganimarta aka ciwo, daga sama kuwa wata fanka ce take juyawa wadda take barazanar fadoma dukwanda ya isheta da kallo..... Tsalle nayi nafada akan katifata wadda batada maraba da kasa sbd tsabar tauri, wata kura ta tashi tareda wasu kwari, suka tashi suna kuka da alama Allah ya'isa sukeyimin saboda nazo na takuramasu... Dan danan nadaga fillow na inda na ajiye chek din, amman abinda nagani shine yayi matukar tadamin hankali, nakara murje idanuwa, a tinani na wai idanuwa nane basu ganemin dai dai ba, nasanya hannu na laluba amman shiru babu chek babu alamarsa.... Nan take maganganun likita suka rinka ziyarar kwakwalwata, "dole sai anyi sauri anyimata aikinnan nanda kwana ukku, idan har aka dauki lokaci ba'ayiba, to zaku iya rasa mahaifiyarku" cikin sauri namike tsaye nasanya takalma na, nafice daga gidan...... 7Part7... Bayan nafice daga gidan ina cikin tafiya nafara tinani " to waye zai dauki wannan chek dinda na aje, bayan babu wanda yasan nayi ajiya agun?" wani bangaren na xuciyata kuma ya shaidamin "kadai koma kakara dubawa" banyi kasa a guiwa ba wurin juyawa, nadauki hanyarda zata kaini gida a saukake... ina shiga nafara bincika ko ina acikin dakin, ina cikin dubawa ne naga wasu takaddu ajikin bango, dasauri nakarasa, abinda nagani shine yayi silar zubar hawayena batareda nasani ba, chek dinda yasmeen tabani ne amman saidai duk an ciccireshi da alama bera ne yaci rabonsa yabar sauran... Fitowa nayi daga gida nakoma bin gidajen mtane wa anda nasani ina fadamasu matsalata domin su taimakamin, atinanina zan iya hada kudin ta wannan hanyar, amman duk wanda natunkara da wannan maganar sai shima yanufoni da matsalar iyalinsa, haka nayini yawo acikin gari amman ba'asamu abinda ake nema ba... magriba nayi nanufi asibiti bantsaya ko inaba sai wurin likita. Shiga nayi office din natarar akwai wasu mutane wa anda suke magana dashi. Wuri nasamu nazauna domin jiransu, jikina duk yayi sanyi hankalina atashe na hada kaina da guiwa inata tinani, muryar likitance ta doki dodon kunne na wanda hakan yayi silar maidoni daga duniyar tinanin da na afka. "inafatan dai ka hado kudinda za'ayi aikin gaba daya?" likita ne yake tambaya ta, nidai bance komai ba, saidai mikewa nayi tareda sanya hannu na acikin aljihu. Kudinda na fiddo shine yayi matukar ba likita mamaki wanda yasanyashi bude hangamemen bakinshi tareda fadar "kanada hankali kuwa?, amfada maka ana bukatar kudi naira dubu dari da ashirin, amman ka kawoman dubu biyu, me za'ayi da dubu biyu?" yakarasa maganarsa wadda take kama da fada. Cikin wata sarkakkar murya nake fada, dan Allah kutaimaka kuyimata aikinnan wlh wa'annan kudin sune kadai ke garemu kuma bamuda kowa agarinnan dan Allah kutaimaka wlh zanbiya kudin koda bayan... Tsaidani yayi da hannunsa, sannan yaci gaba da magana "wannan ka'idace ba'ayin aiki sai anbiya kudi duk irin tsananin ciwonda mutun ke fama dashi" ya ida maganarsa yana kallon fankar da keta faman juyawa makale saman office din domin bayarda iska. Ahaka natashi cikin kyarma nanufi hanyar fita waje, inazuwa bakin kofa naji muryar likitan yana fadar "daga gobe duk abinda yafaru da mahaifiyarka kada kazargi kowa kazargi kanka", kawai ficewa nayi ko juyowa banyiba, haka nanufi dakinda aka kwantarda umma, natarar da ita kwance duk an daureta da wasu karafa wanda suka tokare ko ina daga jikinta, batada damar da zata juya kanta balle tayi wani motsi, koda yaushe idanuwanta suna kallon sama, abinci kam saidai abata mai ruwa ruwa wanda zaya wuce batareda da taba hakoranta wahala ba. Inanan nida khadija har akayi kiran sallar isha'i, natashi nayi alwala nanufi masallaci nayi sallah sannan naroki Allah yafiddamu daga halinda muka tsinci kanmu... Tafiya nike batareda nasan inda zanje ba, duk inda naga taron jama'a sai inje wurin infadamasu matsala ta domin sutaimakamin, cikin dan lokaci kankane nakoma kamar mahaukaci, hatta takalman dake sanye akafata sunyi spanner saboda tsabar tafiya kasa, [11:06PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: 7Part... Hatta takalma na sunyi spanner saboda tsabar tafiya kasa. ina tafiya ina tsayawa aduk inda naga mutane, har Allah yakawoni awurin wani shago, nazo agaban shagon natsaya ina duba jikina yadda nakoma kamar mahaukaci, wata murya naji daga cikin shagon tana fadar kai me kakeyi anan? Ina dubawa sai naga wasu yan samari ne su biyu, karasawa nayi abakin kofar shagon natsaya ina fadamasu matsala ta domin sutaimakamin, sai daya daga cikin samarin yacemin "kai malan dallah wuce katafi inda zaka, wa zakazo kayima karya anan?" sai dan uwan nasa yake cewa, "haba farouq miye haka, idan bazaka iya taimaka maiba ai baikamata kacimar mutunci ba, ko yadda kaganshi haka ai kasan yana bukatar taimako" acikin raina nace lallai wannan bai biyo halin masu irin sunansa ba, duk farouq dinda nasani yanada tausayi tareda son jama'a... Turani naji anyi wanda hakan yasanya faruwar faduwata kasa warwas kaina yakalli sama, daga saman shagon naga anrubuta BIN YUSUF TEXTILE.. Farouq ne ya tureni yana fada cewa muhammad irin wa annan mutanen ba abin tausayi bane yawancinsu duk makarya tane... "meyafaru ne?" wata murya ce mai zaki naji tayi wannan tambayar... Sunkuyar dakaina nayi kasa sannan nafada mata duk abinda ke faruwa, cikin yanayin tausayi take magana "wayyo bawan Allah danyi hakuri bara insayi wasu kaya anan sai mutafi asibitin ko" cikin mamaki nadago kaina naiduba ixuwa gareta, kyakkyawar macece budurwa kuma bawani tsayi garetaba sosai amman bazaka cemata gajera ba... Juyawa tayi tashiga shagon. cikin mamaki naga farouq yanayi mata ladabi kamar uwarda tahaifeshi, "hajiya barka daxuwa me ake so ne, ankawo sababbin kaya daga dubai" cikin raina nace, duniya kenan idan bakada kudi kazama abin wulakantawa agun kowa, bayan tagama sayayyar da zatayi ne tasanya farouq yadaukarmata kayan xuwa cikin mota, sannan tabani umarnin inshigo daga ciki, dukawa nayi na tattara takalmana na matsesu a hammata ta sannan nashiga motar, Dubana tayi kamar zatayi dariya sannan takara dacewa "miye haka? Sanya takalmanka mana" nace hajiya ai kar inbatamaki mota, murmushi tayi tareda fadar " haba kai kamardai wani bakauye sanya takalminka mana, kuma ba sunana hajiya ba, sunana sa'adiya amman zaka iya kirana da (sady)" cikin kwarewa tafizgi mota muka nufi asibiti... Muna zuwa muka kutsa cikin asibiti, sady ta tsaida motarta aguraben da aka tanada domin ajiye motoci, cikin hanzari muka fito daga cikin motar muna takawa akasa domin karasawa a office din likita, ina gaba itakuma tana bina a baya har mukaje batareda wani bata lokaciba akayi magana, nan take tarubuta chek dauke da tsabar kudi naira dubu dari da ashirin arubuce taba likita tareda bashi umarnin agaggauta yima umma aiki, batareda bata lokaciba akashiga da ita domin yin aikin... Part8... Bayan anyima umma aiki da sati guda, tana kwanche akan gado, daga gefenta khadija ce zaune, a gudan gefen kuma nine zaune akan wata kujera dukkanmu babu wanda yayima wani magana saidai kallon dakin mukeyi da mutanenda ke shiga suna fita, sallamar da akayimamu itace tajanyo hankalinmu zuwa inda muryar tafito, inajuyawa muka hada ido da ita! Sady ce take tahowa inda muke ahankali take tafiya kamar tana jin tausayin taka kasa, mikewa nayi tareda yimata sannu daxuwa sannan nabata wuri ta zauna, cikin wata siririyar murya take magana "sannunku ya maijikin" khadija ce tayi carab ta'amsa mata "mai jiki dasauki sosai harma tafara zama dakanta" "Alhamdulillahiai daman haka ake bukata" sady tafada yayinda takeyin wani murmushi wanda yayi matukar fiddo kyawon fuskarta, sannan taduka tayima umma sannu nandai suka gaisa, umma tayimata godiya sosai akan abin alkhairin da tayimana, bayan sady tadauki kamar minti 30 sunata firarsu ita da khadija, sannan tamike sukayi bankwana daniyar zata tafi gida. Tana tafiya nima sai nabi bayanta daniyar inyimata rakiya, ina fita bakin kofa sai nahadu dawani abokina anan natsaya muka gaisa itakuma tawuce gaba... Bayan mungama gaisawa ne muka rabu nikuma nakarasa agun sady, tajingina ajikin bakar motarta kirar 406 prestige, bakaramin kyau sady tayiba alokacin, saboda wasu bakaken kaya ne tasanya irin wanda ake cema after dress, sannan tadaura wani jan kyalle akanta wanda nakasa ganewa shin kallabi ne ko mayafi, ga wasu takalma tasanya daga ganinsu kasan badaga nigeria sukeba, kwalliyar sady tayi dai dai da yanayin da akeyi a garin namu, saboda wani yanayi ne kamar lokacin sanyi kuma kamar za'ayi ruwa, babu rana saidai wani iska iska da akeyi garin yayi lullumi kamar da yamma, amman idan kaduba agogo alokacin zakaga karfe goma na safiya... Bari intakaicemaku anan saboda idan natsaya bayyanamaku komai sai mucinye dan lokacin batareda munyi komai ba. Karasowa nayi agabanta tareda fadar hajiya ranki ya dade, wata harara ta wurgamin tareda fadar "banace kadaina kirana hajia ba?" sannan nadan duka nace ayi hakuri sady baza'a karaba... Dauke kanta kawai tayi tareda fadar "daman nazone infadamaka gobe zantafi abuja kuma ba lallai bane indawo saboda acan zanci gaba da zama gidan kanen mahaifina". Hankalina yayi matukar tashi saboda sady itace tadauki nauyin komai a asibitinnan hatta kudin magani itace take bayarwa, lokaci guda kuma tunanina yajuya acikin duniya, natambayi kaina, ina zansamu kudinda zanci gaba da tafiyar da umma har a sallameta, maganar sady ce tamaidoni daga duniyar tinaninda na afka "amsa wannan chek ne kaje banki kafidda sai kuyi amfani dasu, idan kuma basu isa ba ga number wayata zaka iya kirana" tamikomin wani dan kati mai rubuce da lambarta har adress dinta.... Bansan lokacinda naduka agaban sady ba inayimata godiya, dasauri taja baya tareda fadar "subhanallah Miye haka? tashi tsaye mana" da alamar mamaki karara a fuskarta. Mikewa nayi tareda fadar bansan da irin kalmar da zangodemaki ba sady Hakika samun.... Dagomin hannu tayi alamar inyi shiru hakanan sannan taci gabada magana "kar kadamu na taimakekane saboda Allah bawai saboda wani abuba, kuma taimako yazama dole akanmu saboda manxon Allah yayimana umurni da musulmi yasoma dan uwansa musulmi abinda yake soma kansa, nima wata rana zan iya xuwa wurinka naiman taimako" tana xuwa nan da zancenta naji wani irin faduwar gaba, lokaci guda kuma natina da haleematu wadda itama tafadamin irin wannan kalmar "zan iya zuwa agunka neman taimako" kwalwata taci gaba da maimaita kalamin... Wani bangaren na xuciyata kuma sai yatunomin da abinda yasmeen tafadamin "karikemin soyayyata amana har lokacinda zandawo daga makaranta"... Hannun sady ne naga yagifta akan idanuwa na hakanne yasanya nadawo daga tinaninda nakeyi, "tinanin me kakeyi" tafada tana kallona, babu komai nafada alokacinda najuyo duba agunta... Shigewa mota kawai tayi tareda dagomin hannu lokaci guda kuma takuga ma motar wuta tafice daga asibitin..... A bangaren gidan alhaji jafar muhammad kuwa, Saura wata daya yasmeen tadawo daga makaranta, hakanne yasanya aunty ta tunkari alhaji jafar da maganar tanaso a hada auren yasmeen da danta abba! Tabbas alhaji jafar yaji dadin shawarar da aunty bilky tabayar saboda shi maison xumuncine kuma yanason yan uwansa sosai. Acikin xuciyar aunty bilki kau bahaka abin yakeba, tanada wata manufa can tata daban ta kashin kanta....... [11:08PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: Alkawari 9Part9... Bayan anyima umma aiki da sati guda, tana kwanche akan gado, daga gefenta khadija ce zaune, a gudan gefen kuma nine zaune akan wata kujera dukkanmu babu wanda yayima wani magana saidai kallon dakin mukeyi da mutanenda ke shiga suna fita, sallamar da akayimamu itace tajanyo hankalinmu zuwa inda muryar tafito, inajuyawa muka hada ido da ita! Sady ce take tahowa inda muke ahankali take tafiya kamar tana jin tausayin taka kasa, mikewa nayi tareda yimata sannu daxuwa sannan nabata wuri ta zauna, cikin wata siririyar murya take magana "sannunku ya maijikin" khadija ce tayi carab ta'amsa mata "mai jiki dasauki sosai harma tafara zama dakanta" "Alhamdulillahiai daman haka ake bukata" sady tafada yayinda takeyin wani murmushi wanda yayi matukar fiddo kyawon fuskarta, sannan taduka tayima umma sannu nandai suka gaisa, umma tayimata godiya sosai akan abin alkhairin da tayimana, bayan sady tadauki kamar minti 30 sunata firarsu ita da khadija, sannan tamike sukayi bankwana daniyar zata tafi gida. Tana tafiya nima sai nabi bayanta daniyar inyimata rakiya, ina fita bakin kofa sai nahadu dawani abokina anan natsaya muka gaisa itakuma tawuce gaba... Bayan mungama gaisawa ne muka rabu nikuma nakarasa agun sady, tajingina ajikin bakar motarta kirar 406 prestige, bakaramin kyau sady tayiba alokacin, saboda wasu bakaken kaya ne tasanya irin wanda ake cema after dress, sannan tadaura wani jan kyalle akanta wanda nakasa ganewa shin kallabi ne ko mayafi, ga wasu takalma tasanya daga ganinsu kasan badaga nigeria sukeba, kwalliyar sady tayi dai dai da yanayin da akeyi a garin namu, saboda wani yanayi ne kamar lokacin sanyi kuma kamar za'ayi ruwa, babu rana saidai wani iska iska da akeyi garin yayi lullumi kamar da yamma, amman idan kaduba agogo alokacin zakaga karfe goma na safiya... Bari intakaicemaku anan saboda idan natsaya bayyanamaku komai sai mucinye dan lokacin batareda munyi komai ba. Karasowa nayi agabanta tareda fadar hajiya ranki ya dade, wata harara ta wurgamin tareda fadar "banace kadaina kirana hajia ba?" sannan nadan duka nace ayi hakuri sady baza'a karaba... Dauke kanta kawai tayi tareda fadar "daman nazone infadamaka gobe zantafi abuja kuma ba lallai bane indawo saboda acan zanci gaba da zama gidan kanen mahaifina". Hankalina yayi matukar tashi saboda sady itace tadauki nauyin komai a asibitinnan hatta kudin magani itace take bayarwa, lokaci guda kuma tunanina yajuya acikin duniya, natambayi kaina, ina zansamu kudinda zanci gaba da tafiyar da umma har a sallameta, maganar sady ce tamaidoni daga duniyar tinaninda na afka "amsa wannan chek ne kaje banki kafidda sai kuyi amfani dasu, idan kuma basu isa ba ga number wayata zaka iya kirana" tamikomin wani dan kati mai rubuce da lambarta har adress dinta.... Bansan lokacinda naduka agaban sady ba inayimata godiya, dasauri taja baya tareda fadar "subhanallah Miye haka? tashi tsaye mana" da alamar mamaki karara a fuskarta. Mikewa nayi tareda fadar bansan da irin kalmar da zangodemaki ba sady Hakika samun.... Dagomin hannu tayi alamar inyi shiru hakanan sannan taci gabada magana "kar kadamu na taimakekane saboda Allah bawai saboda wani abuba, kuma taimako yazama dole akanmu saboda manxon Allah yayimana umurni da musulmi yasoma dan uwansa musulmi abinda yake soma kansa, nima wata rana zan iya xuwa wurinka naiman taimako" tana xuwa nan da zancenta naji wani irin faduwar gaba, lokaci guda kuma natina da haleematu wadda itama tafadamin irin wannan kalmar "zan iya zuwa agunka neman taimako" kwalwata taci gaba da maimaita kalamin... Wani bangaren na xuciyata kuma sai yatunomin da abinda yasmeen tafadamin "karikemin soyayyata amana har lokacinda zandawo daga makaranta"... Hannun sady ne naga yagifta akan idanuwa na hakanne yasanya nadawo daga tinaninda nakeyi, "tinanin me kakeyi" tafada tana kallona, babu komai nafada alokacinda najuyo duba agunta... Shigewa mota kawai tayi tareda dagomin hannu lokaci guda kuma takuga ma motar wuta tafice daga asibitin..... A bangaren gidan alhaji jafar muhammad kuwa, Saura wata daya yasmeen tadawo daga makaranta, hakanne yasanya aunty ta tunkari alhaji jafar da maganar tanaso a hada auren yasmeen da danta abba! Tabbas alhaji jafar yaji dadin shawarar da aunty bilky tabayar saboda shi maison xumuncine kuma yanason yan uwansa sosai. Acikin xuciyar aunty bilki kau bahaka abin yakeba, tanada wata manufa can tata daban ta kashin kanta....... [11:10PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: Alkawari Part10... Zaune suke su biyu akan maka makan kujerun dasuke zagaye da falon, aunty bilky ce tareda danta abba tsawon mintuna biyu babu wanda yayi magana a tsakaninsu, kwalbar mentos ce a hannunsa yana kurba lokaci zuwa lokaci yana kallon umman tasa wadda take zaune kamar tana tinanin wani abu... Abba ne yakatse shirun da cewa, umman gani nazo wani abu yafaru ne? yatambayi ummansa lokacinda yake daga kwalbar lemu yana tararawa acikin bakinsa, aunty bilky tayi ajiyar zuciya sannan tafara magana ahankali kamar wadda take magana da mahaifinta, "abba wata magana ce zanfada maka kuma inaso kanatsu saboda baniso asamu matsala acikin wannan aikin", sannan ya gyara zamansa ya ajiye kwalbar lemun dake hannunsa "to umma inajinki" "kasandai yasmeen takusa kammala karatunta, baifi wata daya ba tadawo gida" "eh umma haka naji su yaya usman suna fada" yafada tareda daura kafarsa daya akan daya, "to narigaya nayima alhaji maganar aurenka kaida yasmeen" dasauri ya tube bakin gilashin dake sanye a fuskarksa yafara magana cikin yanayi wanda yake nuna alamar mamaki "umma aurefa kikace" tace eh aure kuma ba yardarka nazo nemaba, nafadamaka ne kawai saboda yakamata kasani, ko kanasonta ko bakasonta ita zaka aura saboda bazaka lalatamana aikinda nadade inayi ba shekara da shekaru" "to umma...." Katseshi tayi da magana "banason jin wata magana taka kaji abnda nafada maka" ta tashi tafice daga falon tabarshi nan zaune yanata karanta wasikar jakki...... Abba mutun ne wanda yataso cikin gata mahaifiyarshi tanasonshi matuka haka ma mahaifinshi, amman abba baidamu da addininsa ba, hatta sallah bazai iya fadamaka yadda akeyintaba, bayada aiki sai bin abokanan banza duk yan tsotse tsotsen nan nazamani babu wanda abba bayayi, saidai kuma duk irin rashin jinsa baya neman mata, hakanne yasa yasmeen tatsani abba jininsu baizo daya ba......... Zaune muke akan tabarma mahaifiyarmu tana a tsakiya daga gefenta kuma khadija ce, dayan gefen kuma nine nake zaune munata fira kamar yanda muka saba, munacikin fira khadija tayima umma wata tambaya "umma wai bamuda wasu yan'uwa acikin garinnan?" tambayarce tasanya dukanmu mukayi tsit umma kuwa sunkuyar dakanta kawai tayi tana kallon kasa batareda tayi wata magana ba, saida khadija takara magana akaro nabiyu "kinji umma bamuda yan'uwa anan garin??" wani nishi tayi wanda bayada maraba da ajiyar zuciya sannan tafara magana "khadija mahaifinku malan bashir badan asalin kasar nigeria bane, kamar yadda yafadamin. Dan wata kasace wadda ake cema (seraliyon) su ukku ne agun mahaifinsu (kakanku) subiyu maza sai mace guda daya. Tun suna yan yara wani fadane ya barke acikin kasar wanda bansan abinda yatada fadanba, lokacin mahaifinku shekararshi biyar, sai yayanshi yanada shekara bakwai, sai yar kanwarsu tanada shekara ukku. Sannan umma tagyara zama tachi gaba da bamu labari.... Ankashe kowa acikin danginsu sukadai ne sukarage sai yawo acikin gari, duk inda zasuje yayan mahaifinku shine yake goya yar karamar yarinyar shikuma mahaifinku yana binsu a baya. Suna cikin wannan halin na uquba, sai Allah yakawo sojojin nigeria daniyar taimakawa, anan aka hada dasu aka kwashe. Daga seraliyon zuwa nigeria sai antsallaka ruwa, lokacinda akaxo wurin kwale kwale za'a hau domin tsallakowa zuwa nigeria, to ananne suka rabu, basu samu damar hawan kwale kwale guda daya ba su ukkun, saidai yayansu yahau shi da yar kanwarsu macen, daman goye take abayansa, sai shikuma mahaifinku aka daurashi akan wani kwale kwalen, tundaga lokacin suka rabu basukara haduwa ba..... Mahaifinku malan bashir awurin mahaifina yayi karatu saboda mahaifina babban malami ne akasar maiduguri, shine yarike mahaifinku yadaukeshi tamkar danda yahaifa saboda yasan bashida iyaye... Nida mahaifinkiu munshaku dajuna tun muna kanana saboda ko makaranta zanje idan batare dashiba to bana zuwa, duk abinda zamuyi tare mukeyi bacci ne kadai yake rabamu, ganin hakane yasanya mahaifina yahadani aure da mahaifinku... Munanan zaune a maiduguri wani fada yatashi, rikichin yan boko haram, wannan fadan ne yayi silar rasa yan uwana hadda mahaifana gaba daya, kuma shine yayi silar dawowarmu anan garin katsina, bamu dade da dawowa ba mahaifinku yarasu yabarmin ku." umma tana zuwa adai dai nan da zancenta sai tamike tashiga daki, bayan wani dan lokaci sai tadawo dawani dan akwati ahannunta, tabude tafiddo wani zobe ta mikomin sannan tacemin "wannan zoben mahaifinka ne yace inbaka a duk lokacinda ka mallaki hankalinka, kuma wannan zoben yanada matukar tarihi a rayuwarka, saboda shikadaine mahaifinku yatsira dashi lokcinda rikicin seralion yabarke, daman al'adar gidansu ce, dukwanda aka haifa sai anbashi irin wannan zoben" tana mikomin nikuwa na kargamashi a hannuna...... Part11... Tana mikomin nikuwa nakargamashi ga hannuna ina dubar zoben, fari ne kirar azurfa, bawata kwalliya ke gareshi ba saidai zanen wani tambari dake a saman zoben, tabbas naji dadin wannan kyauta saboda ko babu komai zanrika tunawa da mahaifina aduk lokacinda nadubi wanga zobe... Ranar alhamis ina tafiya akan hanya da misalin karfe 03:00pm na agogo inata sauri zannufi gida ga rana sai kwalarmin tsakiyar kai takeyi, wata mota ce naga taci birki a gabana, ina karasawa sai naga dreban gidansu yasmeen ne wanda naji suna kira da (dan balya), bude marfin motar yayi tareda fitowa waje muka gaisa, bayan mungaisa ne yake fadamin yasmeen ta kammala karatunta kuma gobe ma zata dawo gida nigeria insha Allahu. Ba karamin dadi najiba maganar da dan balya dreba yafadamin, bayan mungama magana ne yace inhau yaragemin hanya zuwa gida, haka kuwa akayi nashiga muka lula zuwa gida... Zaune suke acikin falo suna shawarwarin yadda bikin yaran guda biyu zaya kasance, Alhaji jafar ne shida uwar gidansa tareda aunty bilky... "Sannan alhaji yadubi aunty bilky yace kinyima abba maganar damukayi dake?" tadan sunkuyar dakanta tareda fadar "eh Alhaji nafadamai, kuma ya amince tareda yimaka godiya akan abin alkhairin da kayimasa" sannan alhaji yayimata nuni da kofar fita daga falon yana fadar "kirawomin abba", mikewa tayi tareda niyar fita takirawoshi, turo kofar da akayi itace ta tsaidata. Abbane yakunno kai batareda yayi sallama ba, dago kanshi dayayi yaga su alhaji shine yasanyashi yin sauri yabude baki yayi sallama, yazo gaban alhaji ya duka yagaishe shi sannan yatashi yanufi hanyar dakinsa, Alhaji ne yakira sunansa tareda bashi umarnin yadawo yazauna yanada maganar da zai fadamai, cikin ladabi kamar mutumin kirki yazo yazauna akan kafet din dake malale a tsakiyar falon, "mahaifiyarka tagayamaka maganar damukayi da ita ko" alhaji yake tambayar abba, alokacinda abba shikuma yake duke yana wasa da gashin kafet din tsakar dakin, sannan yace "eh alhaji tafadamin" to "Alhamdulillahi" alhaji yafada daga bisani kuma yafidda wani iska daga bakinsa yadubi abba yace "idan babu wata matsala ka tashi kawai katafi", sannan abba yamike yanufi hanyar dakinsa, koda yashiga daki sai aunty bilky tabishi, tana shiga batareda yabarta tayi magana ba, yafara tambayarta " haba momy meyasa kukeson hadani da yasmeen ne?" karasowa tayi agabanshi ta dafa kafadarshi, sannan tace zauna dana zanyimaka bayanin komai, sannan tadago kanta tafara magana ahankali yadda na waje bazai iya jin abnda take fada ba "abba kasan Alhaji yanada dukiya sosai, kuma yanada kadarori dayawa a fadin kasarnan" girgiza kai abba yayi alamar "eh hakane" sannan aunty bilky taci gaba da koramai bayani "kaga ni kanwar alhaji ce kaikuma danane nacikina, alhaji kawunka ne, yanxu idan alhaji yakwanta yarasu kana tinanin zamu samu wani kaso daga cikin dukiyarsa? Daga ranarda yarasu babu sauran wani jin dadi dayaragemana duka dukiyarshi za'a tattara aba wannan matar tashi da 'ya'yanta" Nanfa abba yafara murmushi alamar yagane inda mahaifiyar tashi tanufa, daman halin nasu duk daya ne, sannan yadubi ummansa yace "to momy idan na auri yasmeen sai ayi yaya kenan" wata dariyar keta tayi sannan tace "yauwa dana kagane inda nanufa kenan" yadubeta yace "eh mana momy mu duniya ai gaba muka bata ba baya ba, amman wani hanzari ba gudu ba, koda na auri yasmeen alhaji yarasu bawani kason kirki zamu samuba saboda yanada yara maza har guda biyu kuma kinga yasmeen mace ce kasonta dan kadan ne" sannan aunty bilky ta dubeshi tace "to kana tinanin idan ya mutu zamu barsune suma suci gaba dashan iskan duniya?" sannan abba yadan gyara zama yakurama ummansa ido kamar yana neman wani abu akan fuskarta daga bisani kuma yace umma kina nufin... Yayi mata nuni da yatsanshi akan jijiyar dake gefen wuyansa yaja layi zuwa jijiyar dake gudan gefen wuyanshi" sannan ta gyadamashi kai alamar "eh" daga bisani kuma tace, basu kadai bama, duk wanda yatsaremana hanya shima zai bakunci lahira..... [11:11PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: Alkawari Part12... kayana nadauko wa anda nafi jidasu nasanya, nanufi gdansu yasmeen ina tafiya ina sake sake acikin zuciyata, wani sashen nazuciyata kau cike yake taf da farin ciki... Batareda bata wani lokaci ba na isa bakin kofar gdan, nayima malan zayyana mai gadi sallama kamar yadda nasaba, aduk lokacinda nazo gun yasmeen, wurin mai gadi nake tsayawa inyimata waya sannan tafito ta iskeni... Dasauri tafito tanufo inda nike, ni kaina bansan lokacinda namike tsaye ba, amman abin mamaki babu wanda ya iya bude baki yayima wani magana saidai kallon kallo kawai mukeyiwa juna har kimanin tsawon mintuna biyu. Sai alokacin nakauda idanuwana daga cikin idonta, tareda sunkuyar dakaina, nace mata barka da dawowa, sannan tayi wani kayataccen murmushi wanda yakusa fiddani daga cikin hayyacina tareda fadar "yusuf kaine yau agabana?" sannan nima narama murmushinda tayiman, tareda binta muka nufi inda muka saba zama domin fira... Duk wanda yaganmu alokacin yasan muna cikin farin ciki marar misaltuwa, muna cikin firarmu irinta masoya, nacemata darling wlh cikin yan kwanakinnan ina cikin damuwa, tace me yafaru dakai ne? nadubeta nace gaskiya darling wani mafarki na tabayi wai ansaceki...Takuramin ido da alamar mamaki "ansaceni?"... Haba sweety wannan mafarkin shaidan ne kawai ka kwantarda hankalinka.. Sannan nagyara zama tareda fadar shikenan abar wannan maganar... Bara intambayeki mana darling don karwai kiga kinje kasar turawa kindawo nikau haryanxu ko kano banwuce ba, kinsanni malaminkine ko kinaso ko bakiso, nakarasa maganata ina murmushi da alamar wasa a fuskata... Ta kalleni tareda rama murmushinda nayimata, tace "dama ai banyima gardamaba ina saurarenka". Nadan gyara zama nace, minene yafi komi kwarjini a duniya?. Murmushi tayi mai kama da dariya, alamar ta harbo jirgina "haba waye baisan wannan amsarba, ai tun acikin wani film din hausa, na san wannan amsar"... Tana zuwa nan nakatseta ta magana, kenake saurare ki bani amsar kawai ba sai kintsaya yin wani dogon sharhiba... amsarka itace "wata daren 14" ko bahaka bane ". kwarai kuwa wannan haka yake, ashe dai tawan da sauranta... Wani farr tayiman da idanuwa tareda fadar "mikake nufi da saurana?" ina nufin kina da sauran ilimin gargajiya. Nafada tareda nunata da dan yatsa na... ashema! To ni bari inyi maka tawa tambayar... Nakalleta da alamar mamaki nace, harkinada abinda zaki tambayeni wanda bansaniba?.. bari cikamani baki, abinda nakeso intambayeka shine, minene yafi komidadi a duniya?, lokacin nacire hulata nace tabdi! Amma wannan ke kika kirkiro abinki ko... Ta kalleni tace "ko kadan, nima acikin film din hausa najita"... Sannan nadan nisa nace, to indai hakane bari inkokarta ingani, wannan inaganin shine soyayyen naman kaza da yanshila... Kawai tawani bushe da dariya tana tafa hannuwa, "wane irin naman kaza kuma, idan awajenka tanada dadi ai awajen wani batada dadi ko... Sannan nakara cewa, ina ganin amsar shine mutum ya gama da iyayensa lafiya ko?, tayiman wani irin kallo alamar tayi kamu tareda fadar "gaskiya bahaka bane"... Nakara gyara zama nace, to inaganin aurene... ko kadan ba aureneba, wani auren ai bana dadi baneba na wahalane, takarasa maganarta tana wasa da hannunta... Dadai narasa amsarda zanbata sai nace, to ni nabaki gari!, tayi wata dariyar keta tareda fadar "yauwa nima zanrama, kaga nima yanzu nazama malamarka tunda nayimaka tambaya ka gaza amsawa... Natabe baki nace, eh! Kedai nake saurare, kilan ma ko ke bakisan amsar ba... "wannan bakomai bane illa rashin sanin ranar da zaka mutum" takarasa maganarta tanayiman gwalo (tongue)... Nakalleta daga bisani kuma nace, rashin sanin ranar da zanmutu?... "ko kana tababane"... Nadan karkace nace, kumafa gaskiya inajin hakane, domin idan mutum yasan ranarda zai mutu tokullum hankalinsa atashe yake kuma zaita kidayar ranakunsa, kullum yace saura kwana kaza kinga saboda zullumi duk yabi yarame... Tadanyi dariya "to kagani ko"... Muna cikin fira sai ga usman yayan yasmeen yazo zai shiga gda.. Usman yayan yasmeen ne yana bala'in son kanwarsa kuma yana son duk abnda takeso, shiyasa jininmu yahadu dashi cikin dan kankanen lokaci....... [11:13PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: Alkawari Part13..... Usman yayan yasmeen ne yana matukar son kanwarsa kuma yana son duk abnda takeso, haka zalika ya tsani duk abinda zai bakanta mata rai, shiyasa jininmu yahadu dashi cikin dan kankanen lokaci... Bayan mungama gaisawa yashige gd abnsa, nikuma adai dai lokacin nayima yasmeen sallama zantafi gida domin dare yayi, nakarkata kafafuwa na nanufi hanyar fita waje, "my D" yasmeen tafada, wanda hakanne yasa natsaya tareda juyowa alokaci guda na amsa mata da "na am darling", bani numberka, sai inkiraka da anjima, kasan tunda naje makaranta acan nacanza sim, kuma yanzu banmasan inda yakeba, amman nacanza wani sim din... Shiru kawai nayi ina kallonta, daga bisani kuma nace, jiya wayata tafada aruwa kuma nakai agun mai gyara yace bazata gyaru ba.. "Sai tace ok danyi hakuri bara inshiga gida infito". Bayan tatafi ne, narinka tinanin karyar danayi, bayan nasan rabonda inrike waya tun ranarda yasmeen tatafi makaranta, lokacinda nasha bugu awurin yaran aunty bilki, bansaniba ko sune suka dauki wayar ko anan nabarta, oho! Ina cikin wannan tinanin ne nadago kaine dai dai loakcin aunty bilki takaryo kwana, ba karamin faduwa gabana yayiba ganin tanufoni gadan gadan, fitowar yasmeen daga gida shine yayi silar karkata kafafuwan aunty bilki tacanza hanya.... "Ya akayi naga duk kawani canza daga inshiga gda infito" tafada da alamar mamaki karara a fuskarta.. Hannu nasanya namurje idanuwa na daga bisani kuma nace babu komai, kawai nafara jin bacci ne. Sannan tamikomin kwalin waya tace gashinan akwai sim aciki, idan kaje gda kasanyata charge zankiraka da anjima. Nayimata godiya sosai sannan najuya nayi tafiyata..... Aunty bilky kuwa daga nan bata zame ko ina ba sai wurin Alhaji jafar, mahaifin yasmeen, tasanar dashi cewa yakamata afadama yasmeen zabinda akayimata tunda dai yanzu hankalinta ya kwanta, Alhaji baiyi wata gardama ba sbd ya yadda da aunty bilki sosai, kuma ko babu komai, yar uwarshi ce ita kadai taragemai duk cikin danginsu... Batareda bata lokaci ba Alhaji yasa aka kiramai yasmeen yazaunar da ita agabanshi, yafara yimata magana "auta kinga dai babu abnda kika rasa a gidannan kuma babu abnda kika taba nema baki samu ba" ta girgizamai kai tareda fadar "eh dady"... Sannan yaci gaba da magana, "inaso kimani wata alfarma guda, dukda nasan bakitaba yiman gardama ba kuma bazakiso abnda zai janyo gardama tsakanina dake ba" sunkuyar dakai yasmeen tayi tareda fadar "dady naji dadin wannan magana taka tun kafin kafadi abnda kakeso in aikata maka, sbd na dade inaneman abnda zanyimaka wanda zai farantamaka rai sakamakon dawainiyata dakayi tun ina yarinya gashi yau har nakai matsayin da zaka nemi inyimaka wani abu, nagode ma Allah daya zabamin kai amatsayin mahaifi, tabbas nayi dacen iyaye" murmushi alhaji yayi sannan yace "nagodemaki diyata tabbas ina alfahari dake kuma naji dadin wa annan maganganun naki..." Sai alokacin alhaji jafar yazauna akan kujerar dayaketa kai da kawo agabanta yana magana...Bayan yazauna ne yakurawa yasmeen ido daga bisani kuma yayi ajiyar zuciya tareda fadar "auta inaso ne zanhadaki aure da Abba, dan wajen bilkisu"... Hankalin yasmeen ba karamin tashi yayi ba nan take taji komai najikinta yadaina aiki, takoma tamkar gawa, sai idanuwanta dasuka fito waje kuru kuru kamar zasu fado, tana kallon mahaifinta dasu, sannan alhaji yaci gaba da magana "kuma bazamu tsawaita aurenba sbd baza awuce sati biyu ba, hatta gdan da zaku zauna, na tanadarmaku" yakarasa maganarsa yana duban yasmeen, sai alokacin ya fuskanci canji daga fuskarta, "lafiya naga kincanja ko bakisonsa ne?" sannan tayi firgigit tafarfado tareda fadar "dady nayi mamakin maganar ne, aure fa kace". "eh aure mana ai kin isa ko" bai bari takara yin wata magana ba, yace kitashi kitafi kikwanta kinga dare yayi sosai". "Tace to dady" tafada acikin wata murya kamar mai shirin yin yin kuka. alhaji yace "lafiya naji kamar kina kuka?". "a'a dady bacci ne yakeson yaci karfi na". "to kiyi sauri kije ki kwanta" yafada batareda yakalli inda take ba.... Tana zuwa tafada akan gado tana kuka mai kona zuciya wanda ko kararsa ba'aji....... Nikau koda naje gida na tarar da hadiza kanwata ta ajiyemin abincina adaki, banyi wata wata ba nazauna nacika cikina... Bayan nakimtsa ne nakwanta sai naji wayar da yasmeen tabani tanata kara, inadubawa naga anrubuta, "darling" akan secreen din, murmushi kawai nayi nadauka tareda kangawa a kunne na "salamu alaikuma" nafara fada, amman maimakon inji an amsamin sallama sai naji ana sheshshekar kuka.... [11:14PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: Alkawari Part14.... Hanakalina ba karamin tashi yayiba sakamakon kukan danaji yasmeen tanayi, nasan bakaramin abune yafaru ba, dakyar nasamu nashawo kanta tadaina kukan, sannan tafadamin anbnda yafaru. Bansan lokacinda nasaki wayar dake hannu naba. Bayan yan kwanaki kalilan yanayina yacanza gaba daya duk nabi narame na kode, dukwanda yaganni yasan akwai damuwa atare dani. Bangaren yasmeen kuwa itama haka abin yake idan kaganta kamar kabusa mata iska tafadi sbd tsabar rama ko abnci bataci, kuma anyi anyi da ita tafadi abnda ke damunta amman taki fada, saidai duk lokacinda alhaji yatambayeta sai tacemai babu komai. Haka suka kasance har tsawon sati daya... Zaune take acikin falo itada yayanta usman, sunmaida hankalinsu akan makekiyar tv din dake manne ajikin bango, duk wanda yaga yasmeen alokacin zaice kallo takeyi amman azahiri hankalinta baya akan tv din tanacan tana tinanin matsalarda tayankemata walwala da jin dadi. Usman ne yadubeta yana magana ahankali acikin yanayi na tausayi "yasmeen meyasa bazaki fadama dady kinada wanda kikeso ba?" ajiyar zuciya yasmeen tayi, daga bisani kuma taba usman amsa "yaya bazan iya tunkarar dady dawannan maganar ba, kuma kai kanka kasan dady yanada tsaurin ra'ayi, ko na fadamasa bazai canja maganarsa ba" takarasa maganarta tana duban yayan nata tareda wasu yan matan hawaye daketa yar rige rigen fitowa daga cikin idanuwanta... Kauda kanshi yayi sbd bayason ganin ambaliyar hawayenta sannan yaci gaba da magana batareda yadubi inda takeba "yasmeen karki damu, kuma kidaina kuka insha Allahu sai kin auri wanda kikeso "dasauri tazo agabanshi tazauna tana magana acikin yanayi na ban tausayi ga hawaye sai wanke kyakkyawar fuskarta yakeyi "yaya usman dan Allah kataimake ni wlh bazan iya auren kowa ba inba yusuf ba, wlh shi nakeso dan Allah yaya...." Bata karasa maganartaba tadaura kanta akan kafafuwan yayan nata tana zubarda hawaye. Mikewa yayi tareda fadar karki damu nasan abnda zanyi... Daga bayansu kuma aunty bilki ce boye a bayan labile tanajin duk abnda suke fada, saf saf tayi takoma dakinta batareda sunjita ba, tana shiga tadauki wayarta takira danta abba, yayi sauri yazo da gaugawa... Bayan yazo ne take fadamai abnda yafaru tsakanin yasmeen da usman, sannan takara dacewa "yazama dole sai munyi maganin wannan yaron domin zai iya zuwa yakai maganar agun alhaji, dukda nasan babu wanda ya'isa yacanzama alhaji ra'ayi, amman ina tsoron usman sbd shine babban dan alhaji kuma alhaji zai iya sauraren maganarsa, dole sai munyi wani abu acikin gaggawa" bayan ta idarda maganarta ne tazauna akan gadonta, shikau abba yana tsaye agabanta, sai alokacin yacire makeken gillashin dake sargafe akan fuskarsa, yace "umma inaganin da yaya usman zamu fara", mikewa tayi tsaye tana tambayarsa cikin mamaki, "kana nufin mufara aikashi?"."Eh ina ganin wannan itace hanya mafi sauki". "nabar komai ahannunka kuma katabbata kar asamu wata matsala", "angama umma danki bazaibaki kunya ba", yafada yana murmushin mugunta... Wanshekare tunda safe Usman yashirya yanufi gidanmu sbd yanason mutattauna yanda za a bullowa lamarin, baiyi wata wataba kawai yakutsa kai cikin gidan, sbd daman ko baninan yakanzo lokaci zuwa lokaci yagaida umma, hakanne yasa har yasaba da hadiza kanwata, sukan dade suna fira aduk lokacinda yaya usman yazo gidanmu... Yana shiga yatadda hadiza, yatambayeta "ina yusuf?" tace "bayanan" cikin hanzari yabata sako tafadamin "idan yadawo kicemai muhadu a katsina club da karfe hudu na yamma, yanzu sauri nakeyi zantafi office" cikin hanzari yashiga yagaida umma sannan yawuce wurin aiki... Karfe hudu tanayi, na isa katsina club amman banga usman ba, bayan nakirashi awayane, sai yake ceman yanzu yana office kuma ayyuka ne dayawa agabansa, amman injira zai turo kanensa (aliyu) sai yazo yakaini office din, inanan zaune sai ga aliyu yazo, bayan mungama gaisawa ne har zamu tafi sai mukaga wasu mutane sun zagayemu duk sun rufe fuskokinsu dawani bakin abu yadda bazaka iya ganesu ba. Cikin wata kakkausar murya babban cikinsu yake magana "takwalale" me kake jira dashi ne, cikin zafin nama naga daya daga cikinsu ya nufi aliyu, alokacinne nikuma nayi yunkuri domin inshiga gabanshi, amman sai naji wasu bakaken katti su biyu sunyi carab dani, basusha wata wahala ba wurin rikeni sbd daman bawani afki gareniba... Inaji ina gani suka sanyamai wuka aciki. Sannan suka sakeni, suna juya baya sai suka bude fuskokinsu, dai dai lokacin kuma idi mai gadi yafito daga dan dakinsa, suka hada ido biyu dashi... Dasukaga haka sai suka kamashi sukaita bugunsa harsaida yadaina motsi sannan sungumeshi sukayi gaba dashi.. Inanan duke agaban gawar aliyu ga wuka acikinsa narasa yadda zanyi... Hannu nasanya dakyar nazare wukar daga cikinsa, wadda tuni tayi jage jage da jini, adai dai lokacin yan sanda suka shigo... Basu tsaya saurarena ba kawai suka sanyamin ankwa kamar sunkama wani gagarumin dan fashi.... [11:15PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: 15ALKAWARI Part15...... Hannu nasanya dakyar nazare wukar wadda tuni tayi jage jage da jini, inata zare idanu, hankalina atashe sai kiran sunan aliyu nakeyi, ga wukar ahannuna amman nakasa yaddawa kamar ansanya wani abu anmanne hannu na da wukar, adai dai lokacin wasu yan sanda su hudu suka kunno kai, abin kamar hadin baki, da bindiga ahannunsu suna nuna ni da ita suna fadar "you are under arrest". Na daga kafata daya zan mike sai daya daga cikin police din yace "kar kasake katashi daga inda kake, idan har kasaba hakan, bindiga ta bazatai jinkirin shiga cikin naman jikinka ba" yakarasa maganarsa yana matsowa akusa dani. Sai alokacin natina da akwai wuka ahannu na, dasauri nayadda wukar inata zare idanu, nasan babu wanda zai iya fiddani sai Allah... Bayan dan sandan ya ida isowa aguna sai yasanya wani farin kyalle yaduka yadauki wukar tareda fadar "sajen lawal gwanda, sanyamai ankwa" dasauri wanda aka kira da sajen lawal gwanda yakaraso aguna tareda fiddo ankwa daga gefen wandonsa ya kargama man ahannu, dasauri namike ina magana cikin kyarma ina fadar, wallahi bani nakashe shiba, tsawa sajen lawal gwanda yayiman tareda fadar, "banan yadace kafadi haka ba, idan munje can zakayi bayani" basu tsaya saurarena ba, suka tasa keyata gaba izuwa cikin mota bamu zame ko inaba sai sabon gari station... Dukwanda yaji abnda yafaru dani saida hankalinshi yatashi daga abokaina har yan gidanmu..... Alhaji jafar muhammad shine yafara cin karo da labarin, yana zaune a falo yana sauraren radio fm katsina, yaji labarin kamar haka: "dazu dayamma muka samu labarin rasuwar wani yaro matashi mai suna (aliyu jafar muhd) a katsina club, saidai kuma abnda yabaiwa mutane mamaki shine, ankama wanda yayi kisan batareda yaruga ba kuma baiba jami'an tsaro wahala ba wurin kamashi. ga cikakken bayani daga bakin kwamishina of police na jahar" muryar dan jaridar tadauke sannan muryar kwamishina taci gaba da tashi "adazu ne yaranmu suna cikin aiki sai sukaga wata mota kirar golf ta wuce aguje wanda gudun yawuce ka'ida, wannan ne yaba yansanda damar bin wannan mota amman suka kasa cimmata sakamakon wata danja data tsaidasu adai dai round about din kofar kaura, bayan sunsamu sunwuce ne sukabi sawun motar har a katsina club, amman basuga motar ba, ananne suka samu wanisaurayi mai suna yusuf da laifin kisankai dumu dumu... Innalillahi wa inna ilaihirraji'iun alhaji jafar yake fada, sbd baya bukatar wani bayani tunda aka bayyana sunan dansa, kuma aka fadi sunan yusuf amatsayin wanda yakashe shi, sbd yasan yusuf yakangansu tareda usman ko aliyu amman baisan abnda yake kawoshi gidansa ba.. Dasauri alhaji ya yadda radion dake hannunsa yana fadar "me dana yayimaka zaka kashe shi? Wlh kaima sai ankasheka ko dan gidan uban wanene kai" ya ida maganarsa kamar mai sabbatu. Dan lokaci kankane gidan alhaji ya hargitse... Dasauri yasmeen tadauki waya takira yayanta usman tashaidamai abnda ke faruwa, tana gama fadamai yace "ina wannan ba gaskiya bane, yusuf bazai iya kashemin kane ba" daga dayan bangaren kuma Yasmeen tafada "wlh yusuf bazai iya yin kisan kai ba, kuma ko halinsa ne nasan bazai iya kashe dan uwana ba" ta idarda maganarta tareda sanya hannu ta share hawayen dake gangarowa akan fuskarta... Suna gama waya itada yayan nata, shikuma yanufi gidanmu ko sallama baiyiba ya kutsa kai aciki, yana shiga yatararda hadiza kanwata tagama sallar isha'i, cikin rudu yaci gaba dajero mata tambayoyi, "hadiza kinji abnda yafaru? Ina umma? Hadiza idan dagaske ne ya..." tsaidashi tayi bata bari yaci gaba da magana ba, itama ta watsomai tata tambayar "meyafaru ne yaya usman lfy?" jin tambayar datayimai shine yabashi tabbacin batasan abnda yafaru ba, dasauri yamike yanufi dakin umma, hadiza ma mikewa tayi tabiyoshi tana tambayarsa amman ko kadanma baisan abnda takeyiba, yanata Alla Alla Allah yasa umman yusuf bataji ba, sbd yasanta ma abociyar jin radio ce... Yana shiga dakin yatarar da umma yashe akan gado ga radion ta nan tayi dai daya a tsakar daki duk ta watse, battery daban marfi daban hatta area din radion ta karye... Hankalin hadiza ba karamin tashi yayiba da taga umma acikin wannan halin, dandanan tafice waje dagudu ta debo ruwa ta watsama umma a fuska, wanda hakan yabata damar farfadowa daga suman datayi, sannan takamata tazaunar da ita, hawaye na kwarara a idanuwanta, hadiza takalli usman tace "dan Allah kufadaman abinda ke faruwa" amman babu wanda yabata amsa, sai kuka kawai sukeyi usman da umma, sai akaro nabiyu datayi magana hade da kara tareda kuka cikin wata murya mai gunza "dan Allah ku fadaman" sannan ta sauko da muryarta tana magana ahankali "ko yaya yusuf ne yarasu" ta idar da maganarta acikin wani yanayi wanda idan kaganta dole tabaka tausayi...... [11:16PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: ALKAWARI Part16.... Sai akaro nabiyu datayi magana hade da kara tareda kuka cikin wata murya mai gunza "dan Allah ku fadaman" sannan ta sauko da muryarta tana magana ahankali "ko yaya yusuf ne yarasu" hadiza ta idar da maganarta acikin wani yanayi wanda idan kaganta dole tabaka tausayi, amman still su umma basu bata amsa ba, ganin haka ne yasa hadiza zubarda hawaye masu radadi a fuskarta, takuma tambayarsu a karo na ukku "ina yaya yusuf din yake?". Sai alokacin umma tayi ajiyar zuciya tareda fadar "(Allahumma la sahla illa ma ja'altahu sahlan, wa anta taj'alul hazna iza shi'ita sahlan). Yanzu ina yusuf din yake?" umma tafada tana kallon usman, "yanzu yana hannun hukuma domin sai anyi bincike akan lamarin" usman yafada... Sannan umma tajuya agun hadiza tana zubarda hawaye tana magana kamar wadda ta tashi daga bacci "hadiza yayanki ya jamana bakin duniya yayimana tabon da bazai taba bacewa ba aduniya, ankama yayanki da laifin kisa yanzuma yana hannun hukuma.." dasauri hadiza tamike tsaye kamar a tsikareta ta daura hannuwa abisa kai tana fadar "inna lillahi wa inna ilaihi raji'un, Allahumma ajurni fi musibati wakhlifli khairan minha" dasauri kuma tadurkusa agaban usman tana fadar " wlh usman ba yaya yusuf bane, yaya bazai iya kashe maka dan uwa ba, wlh ko kare bazai iya kashewa ba, dan Allah ka yadda" takarasa maganarta tana wani irin kuka kamar wadda aka aiko mata da rasuwar uwarta da ubanta, sannan usman yamike tsaye yana fadar "nima nasan yusuf bazai iya aikata hakan ba, amman kuyi hakuri yanzu yana hannun hukuma ana gudanar da bincike akan lamarin" a hakadai usman yasamu yashawo kan hadiza da umma, tareda fadar yanzu zaije police station din domin jin abnda ke tafiya... yana fita bai zame ko inaba sai police station inda yanemi a fiddomai yusuf, baisha wata wahala ba wurin ganina sbd yasan mutanen wurin, "yusuf ya akai haka tafaru miye gaskiyar lamarin?" yakarasa maganarsa yana kallona da alamar mamaki a fuskarsa. Wasu hawaye ne masu zafi suka gangaro akan fuskata, ina magana cikin sarkakkar murya, wlh usman banine nakashe aliyu ba, bani nakashe shi ba wlh. Lokacin usman yadafa kafadata shima da alamar kuka a idonsa, yana fadar "karka damu yusuf nasan bazaka iya aikata hakan ba, kuma ko zaka iya nasan bazaka iya kashemin dan uwaba, in Allah ya yadda sai kafita daga wannan kangin" sannan yagyara zama yaci gaba da magana yana tambayata "fadamin yadda abin yafaru", dai dai lokacin ne mukaji muryar wani police a bayanmu yana magana "lokacinda oga yadibar maku yayi, harma kunkara minti biyar". Mikewa kawai usman yayi yana fadar kar kadamu bara intafi, insha Allahu komai zaitafi lfy lau kuma sai angano dukwanda yakeda sa hannu aciki" yajuya yatafi, nikuwa akayi ciki dani..... Daga nan usman ya falli mota yanufi gidanmu, yana shiga yatadda su umma sunyi jugum jugum kowa yayi tagumi kamar masu zaman gaisuwa, yana shiga umma tayo kansa tana tambayarsa "ina yusuf din? Dagaske shi yayi kisan?" "a'a umma bashine yayi ba", "yanzu ansakoshi ko?" takuma tambayar usman ,Jingina yayi ga bango daga bisani kuma yace "babu wata hujja wadda zata bayyana hakan awurin hukuma dole sai anyi bincike akai" zaunawa umma tayi kamar wadda aka yadda akasa bakinta yanata mai maita "qadaru lillahi wama sha a fa'al"..... Bangaren su aunty bilki kau suna can suna murna domin hakarsu ta cimma ruwa, wannan karen ma zaune take acikin daki itada danta, "nayi mamaki da har yau kwana biyu amman alhaji bai shigarda kara kotu ba" abba ne yake magana yana kallon mahaifiyarsa, "haba yaufa kwana biyu ko sadakar rasuwar aliyu ba ayiba yaza ai yashigar da kara, ai sai anyi kwana ukku sannan" ta idar da maganart lokacin da take ajiye kofin dake hannunta, daga bisani kuma tace "amman fa wannan game din yanada dadin kallo saboda gidannan rabuwa zayayi kishi biyu, alhaji da matarsa daban, usman da yasmeen suma jam iyarsu daban, shi Alhaji zai hakikance ne sai ankashe wanda yakashemai yaro, usman kuma zaiyi kokarin kare abokinsa yusuf saurayin yasmeen, sbd ya yadda dashi yasan bashine yayi wannan aikin ba, amman kuma haryanzu alhaji baisan abnda usman da yasmeen suke shukawa ba", aunty bilki ce take magana tana wani murmushin mugunta, sanna abba yayi magana "momy amman ni ina gani yakamata alhaji yasan usman da yasmeen suna kokarin kange yusuf, kinga sai yasan matakin da zai dauka akansu, sbd munaso ayi shari ar nan cikin gaggawa batareda bata lokaci ba, ayankemai hukunci shima yabi aliyu, kinga idan akai haka dole yasmeen zata amince da aurena batareda wata matsala ba sbd ankashe wanda take so", dasauri aunty bilky tagyara zama tace "eh gaskiya haka yakamata muyi amman bai kamata mufada ma alhaji wannan maganarba, shi yakamata yagani da idonsa" takarasa maganarta lokacinda take jingina akan kujerar datake zaune, "ta yaya zamu bullo ma abin" abba yatanbayi aunty bilky, "wannan karen, kabar komai a ahnnu na, nasan yanda zanyi" tafada !tareda mikewa tsaye tanufi hanyar fita waje........ [11:19PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: 17ALKAWARI Part17..... Yau kwana hudu kenan da faruwar wannan al'amari... Zaune nike nasanya kaina acikin kafafuwana inata tinanin duniya dakuma tinanin wannan al'amari wanda ya yankemin jindadi da kwanciyar hankali tareda na dangina... "taso kabiyoni muje ga yan uwanka nan sunzo ganinka" muryar wani gandroba ce ta doki dodon kunnena, faruwar hakan ne yayi silar tsinkewar tinani na, banyi gardama ba nayi kamar yanda ya umurta natashi nabiyoshi, zuciyata tana tinanin suwanene kuma sukazo gurina, wani bangaren na zuciyata kuma yana rayamin usman ne yazo aguna sbd nasan shine yake zuwa adai dai irin wannan lokacin akowace rana. Kai tsaye nawuce inda aka tanada domin ziyartar masu laifi, ina shiga yasmeen idona yafara hangowa wadda ta kode ta rame kamar wadda ta shekara tana ciwo batareda ankulata ba, duk wanda yaganta yasan tana cikin tashin hankali, idan kuwa mutun yadubi idanuwanta sai ya fahimci ta kulla abota da kuka, saboda ilahirin idanuwanta duk sun rikida sunyi jajur sbd zirga-zirgar da hawaye keyi acikinsu, daga gefenta kuma mahaifiyata ce zaune idan kaganta sai karantse bata taba sanin wani abuba waishi kwanciyar hankali, hatta farar fatar jikinta tayi jajur kamar wadda ta shekara acikin rana, dayan gefen kuma hadiza ce nagani a tsaye itada usman, ina ganin hadiza nafahimci tana cikin mawuyacin hali, fuskarta da idanuwanta duk sun kumbura. Tunkafin inkarasa agunsu naji wasu hawaye suna gangarowa akan fuskata batareda izni na ba, dakyal nakarasa agaban umma nadurkusa nagaisheta... Bayan mungama gaisawa ne usman yadubeni cikin damuwa yana fadar "Alhaji ya shigar da kara a kotu nan bada dadewa ba" sannan yayi wani nishi mai kama da ajiyar zuciya daga bisani kuma yace "karka damu yusuf zansamar maka lauya wanda zai kareka kuma za asamu nasara insha Allahu" rufe bakinsa shine yayi dai dai da shigowar alhaji jafar tareda aunty bilki, ba karamin tashi hankulanmu sukayiba zuwan alhaji jafar da aunty bilky, musamman ma usman da yasmeen yadda suka kidime lokaci guda zufa tayomasu lale marhabin. Usman ne yayi karfin hali yakarasa agaban Alhaji tareda rusunar dakanshi kasa yaci gaba da magana muryarshi tana sarkewa "Alhaji barka da yini", (fassssss) karar mari ce tagarwaye wurin, maimakon amsa gaisuwa daga bakin alhaji, tabbas usman yaji zafin marin sbd har tangadawa yayi kamar zaifadi kafin yabude baki yace wani abu, Alhaji yaci gaba da magana yana nunashi da dan yatsa cikin zafin rai "kai usman ashe kai shasha sha ne bansani ba, me kakeyi awurin wanda yakashe maka dan uwa, me kake nufi ne" shirun da Alhaji yadanyi shine yaba usman damar yin magana, "wlh dady bashine yakashe aliyu ba wlh ba...." saukar hannun alhaji akan fuskar usman shine yayi silar hana usman ida maganar, sannan alhaji yaci gaba da magana "to wlh baka isaba, kuma babu wanda ya isa yahana akashe wannan yaron ko dan wanene" yakarasa maganarsa yana nuno ni da danyatsa. Wannan maganar da alhaji yafada ba karamin tada hankalin mahaifiyata yayiba sbd tasan babu wanda ya isa yashiga gaban Alhaji Jafar saidai ikon Allah, dasauri umma tazo ta durkusa agaban Alhaji jafar tana magana hade da kuka "dan Allah alhaji kataimakeni kayimana rai wlh shikadai ne yaragemin a duniya sai kanwarsa bamuda ko..." dagama umma hannu yayi tareda fadar "kinfini sanin dadin haihuwar ne kika bari danki ya hallaka nawa? Ke wlh ko dan dan shugaban kasa ne yakashemin yaro shima sai ankashe shi" dasauri kuma yajuya yafice, su aunty bilki suka rufamai baya, suna fita sai wasu bakaken mutane suka shigo su biyu katti sukayo kan usman tareda rikemai hannuwa daniyar tafiya dashi ko yaki ko yaso, cikin mamaki yake tambayarsu "me kuke nufi ne? Kunsan koni waye?" yana rufe bakinsa sai ga alhaji yadawo, "ni nasanyasu kuma bazaka kara fitowa koda kofar gida ba harsai angama shari'a, ko asiri wa annan mutanen sukayimaka saidai yatsaya akanka amman nafi karfinsu" alhaji yafada cikin fushi, nan take bakaken mutanen nan sukayi waje da usman, yana kallona yana zubarda hawaye... Hadiza ce takaraso aguna tana kuka tana fadar yaya yusuf munshiga ukku yazamuyi kenan" sunkuyar da kaina kawai nayi ina zubar da hawaye sbd banida amsar da zanbawa hadiza. Maganar umma ce tayi silar dago kaine "ku kwantar da hankalinku babu abnda zai faru insha Allahu, kudauka wannan jarrabawa ce Allah yakeyimana, yakamata mudaure muci wannan jarrabawar kota halin kaka" umma ce take magana daniyar kwantarmana da hankali, amman zuciyarta cike take fal da damuwa tareda tashin hankali wanda gayanan karara a fuskarta, sannan tadafa kaina tace "yanzu babu abnda yaragemana sai addu'a" sannan nadago kaina nace "umma yaushe za'ashiga kotun ne?" ajiyar zuciya tayi sannan tace "ranar litinin 16 ga wannan watan" [11:21PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: ALKAWARI Part18.... Ranar litanin 16-6-2014, kotun tacika makil da mutane maza da mata. bayana wasu police ne guda biyu wa'anda suka sanyani gaba duk idan nadaga kafata suma sai su daga tasu, haka muke tafiya, hannuwana daure suke da ankwa ina tafiya amman kaina a duke inata zubar da hawaye, nakasa dago kaine inkalli mutanen dake wurin sbd tsabar kunya da bakin ciki, "wai yau nine a kotu da laifin kisa" nafada acikin zuciyata tareda takaici acikin raina, rakani sukayi har acikin wani dan akurki wanda yaboye duk ilahirin jikina amman daga kirji na zuwa kaina duk awaje suke. Bayan kowa ya maido hankalinshi akanmu sannan alkali yadubi wani mutun wanda yake zaune akan wani teburi, daga mai kai kawai alkali yayi, naga mutumen nan yamike alamun ya fahimci abnda alkali yake nufi, sannan yadukar dakansa yaci gaba da karanto wata takarda dake hannunsa "zamu shiga shari'a ta biyu awannan rana, akan kisan da akayiwa aliyu jafar muhammad, wanda ake zargin yusuf ahmad muhammad da aikatawa" sannan yakoma akan teburinsa yazauna. Alkali yadukar dakansa yayi wasu yan rubuce-rubuce da alkalaminsa sannan yadago kansan yadubi sashen wasu mutane wa'anda daganinsu kasan lauyoyine. Daya daga cikinsu yatashi dawasu bakaken kaya na lauyoyi, yamike yaci gaba da magana "sunana barista Auwal mu'azu rimaye, lauya mai zaman kansa daga chamber din M.A Bello & co. Kano. Nine lauya wanda yake kare hakkin wanda aka kashe" sannan yakoma yazauna. Nikam a lokacin zuciyata sai dukan tara tara takeyi saboda a'iya sanina banida wani lauyan dazai kareni, kamar ance indago kaina, ina dagowa nahada ido da umma tana zaune ita da hadiza sai faman zubar da hawaye sukeyi, mantawa nayi da halin danake ciki sakamakon tinani da tausayin su umma daya kamani, tabbas suna cikin damuwa wadda tafi tawa, da alama sunfini shan azabar faruwar wannan lamari. Alkali daya gama rubuce rubucensa yadago kansa a zatonsa zaiji lauya wanda ke kare wanda ake kara yagabatar dakanshi, amman yaji shiru. Hakan shine yabashi damar buda baki yayi magana a karo na farko tunda muka shigo, "lauya wanda yake kare wanda ake kara" haka kawai yafada yana kallon bangaren da lauyoyin suke zaune, kafin ya rufe bakinsa aka turo kofa dakarfi kamar za'a balle ta, hakane yayi sanadiyar karkata idanuwan alkali tareda hankalin duk mutanen dake cikin kotun domin ganin wanda yake shigowa, ba karamin mamaki nayiba danaganta acikin kayan lauyoyi wa'anda sukayi mata kyau matuka kamar daman dan ita akayisu Karasowa tayi gaban alkali batareda bata lokaci ba muryarta taci gaba da tashi, "sunana barista sady al-mustapha, lauya mai zaman kanta, nice wadda take kare wanda ake tuhuma" alkali yakalleta kamar zai fadamata wata magana amman sai yayi shiru yadukar dakansa yaci gaba da yan rubuce-rubucensa ganin haka ne yasa barista sady tanufi wurin zama tazauna, daga bisani kuma alkali yadago kansa "idan akwai wanda yake bukatar tambayar wanda ake tuhuma, zai iya farawa ayanzu" yafada yana mai duban lauyoyin. Barista auwal ne yamike "idan kotu tabani dama inaso inyima wannan mutum wasu tambayoyi". "Anbaka dama" alkali yafada atakaice. Sannan barrister yakaraso agabana "malan zaka iya bayyana ma kotu sunanka" sunana yusuf ahmad muhammad, nabashi amsa atakaice, "ina fatandai kasan abnda yasa aka shigo dakai anan" yakuma tambayata, dagamai kai nayi alamar "eh", "naji sunan naku daga karshe kamar iri daya dana marigayi, ko zaka iya fadama kotu dangantakarka dashi marigayi aliyu?" barista auwal yafada, "babu wata dangantaka ta jini tsakanina dashi" nafada muryata na sarkewa, sannan barista yagyara tsayuwarsa "sbd babu wata dangantaka tsakaninka dashi shiyasa ka kashe shi kenan..". "Objection ya mai girma mai shari'ah! Yakamata mai tambaya yakiyaye kalamansa sbd haryanzu bincike akeyi ba'a tabbatarda wanda yayi kisan ba". "mai tambaya sai yakiyaye" alkali yafada atakaice. Barista yakuma tambayata "yusuf lokacinda aka kashe aliyu, ku nawa ne awurin?" babu kowa mukadai ne, nabashi amsa atakaice, sannan yaci gaba da magana "babu kowa! Kana nufin shi yakashe kanshi kenan koko wukar ce ta taso dakanta takashe shi?" sady tamike "objection ya mai shari'ah! yakamata mai tambaya ya sassauta kalamansa na tsoratarwa akan wanda ake tuhuma sbd bako ne a shiga kotu...", barista yayi sauri yatarbi hanzarinta da fadar "yakamata kotu tayi watsi da korafin abokiyar aikina, sbd bankauce hanya ba, ina akan hanya tane ta kokarin gano gaskiyar wannan lamari", "mai tambaya bai kauce hanya ba, zai iya cigaba da tambayoyinsa" alkali yafada, sannan sady tazauna fuskarta da alamar damuwa.. Barista na gama tambayarsa yayi godia ga alkali yazauna. Alkali yadukar dakai yayi yan rubuce-rubuce sannan yadago kansa, "akwai wanda keda wata tambaya" alkali yafada, shirunda akayi ne yasa alkali ya disa aya akan takardarsa, "Sakamon rashin isasshen lokaci kotu ta daga wannan kara zuwa daya ga watan janairu shekara ta dubu biyu da shahudu" sannan yabuga wata guduma akan tebur tareda mikewa tsaye. kooootu!!..... [11:36PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: 19ALKAWARI Part19.... Barista yace "babu kowa! Kana nufin shi yakashe kanshi kenan koko wukar ce ta taso dakanta takashe shi?" sady tamike "objection ya mai shari'ah! yakamata mai tambaya ya sassauta kalamansa na tsoratarwa akan wanda ake tuhuma sbd bako ne a shiga kotu...", barista yayi sauri yatarbi hanzarinta da fadar "yakamata kotu tayi watsi da korafin abokiyar aikina, sbd bankauce hanya ba, ina akan hanya tane ta kokarin gano gaskiyar wannan lamari", "mai tambaya bai kauce hanya ba, zai iya cigaba da tambayoyinsa" alkali yafada, sannan sady tazauna fuskarta da alamar damuwa... Barista yakuma dubana yasake maimaita tambayar dayayiman akaro nabiyu, "yusuf kana nufin shi yakashe kanshi koko wukar ce ta taso dakanta takashe shi?". Wasu hawaye ne suka gangaro afuskata kyarma takamani, naci gaba da magana kamar dan koyo, wlh wasu mutane ne nima ban sansuba kawai ganinsu nayi sun zagayemu. nakarasa maganata ina kallon barista auwal a tsorace. Wani dan gajeren murmushi yayi sannan yajuya agun alkali yaci gaba da magana "yakamata kotu tayi duba izuwa maganganun wanda ake zargi, saboda bayaninsa nabiyu ya karyata bayaninda yayi abaya, dafarko cewa yayi babu kowa subiyu ne kadai lokacinda wannan abu yafaru, yanzu kuma yace wasu mutanene sukayi abin, wannan yana nunamana babu gaskiya acikin zancensa, dawannan kadai ya isa kotu tayima wannan mai laifi hukunci na daidai da laifin da ya aikata". Barista auwal yana zuwa nan dazancensa sai yayima alkali godiya sannan yakoma mazauninsa yazauna. Bayan barista auwal yazauna sai barista sady ta mike tareda fadar "ina neman izni da kotu tabani damar yin magana da wanda ake tuhuma" "anbaki dama" alkali yafada yana dubanta. Tasowa tayi tayo tattaki izuwa gurina sannan tace, "sannu malan kaji, da alama kana cikin damuwa sosai, kuma ko shakka babu ka taka sawun barawo wanda hakan ne yayi silar shigar dakai cikin mawuyacin hali, amman inaso ka kwantar dahankalinka kuma kasani nan kotu ce mai adalci baza'a taba yankema mutun hukunci ba matukar bashine ya aikata laifinda ake zarginsa dashi ba, inaso kafidda duk wata damuwa aranka, ka kaddara wannan nadan wani kankanen lokaci ne kafin agano wanda yayi wannan aikin" sady tafada tana kallona, sannan na girgiza kai alamar na gamsu, cikin dan kankanen lokaci sady tashigar da kalaman dasukayi silar kwanciyar hankalina acikin maganganunta, sannan takalleni atsanake taci gaba da magana "malan yusuf ko zaka iya fadamana wannan ko zuwanka na nawa ne akotu?" a'a bantaba zuwa kotuba, nabata amsa atakaice, "shiyasa naga duk katada hankalinka hatta sunanka ma kakasa fada dai dai sbd fargaba" tafada fuskarta asake kamar wadda take shirin yin murmushi, sai alokacin natina da kwamacalar danayi, sunan danabawa kotu lokacinda barista auwal yatambayeni. Maganar barista sady ce takatseni daga tinaninda nakeyi "yanzu naga hankalinka akwance, zaka iya fadama kotu sunanka?" ta tambayeni. Sunana yusuf bashir muhammad, nafada da kwarin guiwa. Cikin hanzari barista auwal yamike tareda fadar "Objection Ya mai girma mai shari'ah yakamata kotu taduba tagani kuma tayi gaggawar yanke hukunci, sbd tundaga maganar farko har karshe babu zancen gaskiya acikin lamarinsa, shiyasa har sunansa yakasa fada dai dai..." yana zuwa daidai nan dazancensa, abin kamar hadin baki sai muryar barista sady taci gaba da tashi "yakamata kotu tayi duba izuwa maganganun abokin aikina wato barista auwal, idan kotu taduba zata fahimci wannan ba korafi bane yayi, saidai yanabada umurni ne ga kotu domin tayi gaggawar yanke hukunci batareda wani kwakwkwaran bincike ba, idan kuma korafi ne to yakamata kotu tayi watsi da korafinsa, sbd wannan kuskurenda wanda ake tuhuma yayi afarko yanada nasaba da kalamanda aka rinka furtamai na tsoratarwa tun afarko, shiyasa duk hankalinshi yatashi kuma gashi baisaba shiga irin wannan yanayinba" tana zuwa nan da zancenta sai tajuyo akaina tareda tambayata, "malan yusuf ko kataba tsintar kanka acikin irin wannan halin a baya?" girgiza mata kai nayi tareda fadar a'a, sannan tajuya agun alkali taci gaba da magana "ya mai girma mai shari'ah yakamata kotu tayi duba kuma tayi adalci akan wannan bawan Allah wanda baitaba aikata wani mummunan laifiba, ko hukuma tasan da haka, tayaya zai iya kashe mutun, yakamata kotu taduba tagani ayayinda zata zartar da wannan shari'ah"... bayan tagama maganarta ne sannan tayi ma alkali godia, takoma wurin zamanta tazauna, yayinda alkali shikuma yadukufa yanata rubuce rubucensa, bayan yakammala ne sannan yadago kansa tareda fadar"Sakamon rashin isasshen lokaci kotu ta daga wannan kara zuwa daya ga watan yuli shekara ta dubu biyu da shahudu, kuma kotu tana bukatar lauyoyin kowane bangare suzo mata da kwararan hujjoji a zama na gaba" sannan yabuga wata guduma akan tebur tareda mikewa tsaye. kooootu!!..... [11:36PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: 0ALKAWARI Part20 Gaba daya naga kowa nacikin kotun yamike yana niyar fita waje idan kacire umma da hadiza sai barista sady, sune kadai azaune suna kallona cikin damuwa, police dinda suka kawoni sune suka kuma tasa keyata gaba domin fita daga kotun, cikin zuciyata nike tinani wai yanzu komawa za'ayi dani gidan maza yayinda kowa zaya nufi gidansa, ashe zamana bai kareba acikin wannan kazamin wuri... Ta gabansu umma muka wuce muna kallon juna, da alama kowa yanada maganarda yakeso yafurta amman taki fitowa, saidai motsi kawai da bakinmu yakeyi idanuwanmu kuwa sai zubarda hawaye suke, Hadiza ce tabiyo bayanmu dagudu tana kwalamin kira cikin shakakkar murya amman ina, kafin takaraso agunmu har anjefani mota anyi gaba, tsayawa tayi tadafe kai tana kallon motar harsaida taga tadaina ganinmu, sannan barista sady tazo ta lallasheta tareda bata hakuri sannan suka tafi, tattaki sukayi zuwa inda umma take daga bisani kuma sady tagaida ta, sai alokacin umma tagane ko wacece agabanta "sa'adiya daman kece" umma ta tambayi sady da fuskar mamaki, girgiza kai barista sady tayi tareda fadar "eh nice umma" "kiyi hakuri banganeki ba naga kinsha bakaken kaya, daman aikinki ne wannan" umma takuma tambayar sady tana kallonta, eh umma yanzu kushiga inkaiku gida sannan" sady tafada lokacinda take nuna wata farar mota dake gefensu, tattaki sukayi zuwa wurin motar sannan sady tabude ma umma kofar baya hadiza kuwa tazagaya tashiga gaba, batareda bata lokaci ba ta fizgi motar suka hau hanya... Tafiya suke ahankali cikin kwarewa, babu wanda yakema wani magana acikinsu, dukansu sun dunguma zuwa duniyar tinani... "Umma ya akai har haka tafaru tunfarko ba'asanar dani ba" sady ce tayi magana lokacinda tamaida dubanta zuwa ga umma, daga bisani kuma tamaida hankalinta akan tukin datakeyi. "Wlh kaddara ce idan Allah ya tsara ma bawa abu, babu yadda za'ayi ya tsallake" umma tafada daga bisani kuma tace "kuma keda kika tafi abuja, ta yaya zamu ganki". "Hakane! nima nasamu lbrn faruwar lamarinne lokacinda nashigo garin a daren jiya" sady tafada... Haka dai sukaci gaba da magana akan lamarin har suka isa gida, bayan ta kaisu gida itama tawuche nasu gidan domin tinanin ta yadda zata bulloma lamarin... Zaune nike jingine ga bango nikadai acikin dakinda aka kulleni sai tinani nakeyi, "kafito ana son ganinka" muryar wani bakin gandroba ce tadoki dodon kunnena itace tayi sanadiyar dawo dani cikin hayyaci na.. Tasowa nayi nabiyoshi tinkis tinkis, har wurinda nasaba zuwa idan akazo gani na. Barista sady ce nagani zaune akan wani tan benci. tabbas nayi mamaki sosai yadda naga sady ta bayyana amatsayin lauya, alokacinda nike neman taimako takowane hali "Yusuf ya akai wannan abin yafaru kuma miye gaskiyar lamarin" sady ta tambayeni lokacinda tasanya hannu acikin jikka tadauko biro dawani dan littafi, wlh sady bani bane, nafada ina kallonta, "tabbas nasan bakaibane, amman zaka iya tuna yadda abin yafaru?", sannan nagyara zama nafada mata abnda yafaru tundaga lokacinda usman yace yana nemana har lokacin afkuwar wannan abu, bayan nagama koramata bayani sannan takalleni tareda fadar "kuma cikin mutanenda sukayi kisan bazaka iya gane koda mutun dayaba?", gaskiya bazan iya ganesuba sbd duk sunrufe fuskokinsu. "shikenan inaso ka kwantar da hankalinka kuma insha Allahu zaka fita daga zarginda akeyima... Zaune suke su biyu akan wasu yan fararen kujerun roba, sai table a tsakiyarsu daga samansa kuma drinks ne da wasu yayan itatuwa, "momy banyi zaton za'ayi zama biyu ba ashari'ar nan" abba yafada lokacinda yake bulbular wani lemu cikin cup, "ko zama goma za'ayi ai doledai sai anyankemai hukunci sbd baza ataba gano wa anda sukayi aikinba" aunty bilky tafada tareda jingina akan kujerar datake zaune, sannan takara dacewa "ina fatandai lokacinda wannan abu yafaru ko tsuntsu baya gurin" tafada tareda yin kasake tana kallon dan nata, "haba umma ai babu kowa awurin sai wani mai gadi, shima ba agabanshi akayi aikinba amman yaga fitowarmu" dasauri tamike a fusace "kai bakada hankali, me kake fadamun?" aunty bilki tafada acikin tsawa, "haba momy kwantar da hankalinki ai, bamubar wurinba saida muka rufe bakinshi bazai kara magana ba har abada, sbd saida mukaimai bugunda bazai iya wuce hour guda yana lumfashi ba, sannan muka jefashi ruwa" abba yafada lokacinda yake ajiye cup din dake hannunsa, zaunawa tayi tareda yin wata gawurtattar ajiyar zuciya sannan takara dacewa "amman dukda haka kunyi kuskure sbd kamata yayi ku kasheshi dakanku bawai yamutu dakanshi ba, idan yanada sauran kwana agaba ai kaga zai iya tashi, kuma daya tashi kaima kasan sauran basai nafadamaka ba" takarasa maganarta tana kallon abba afusace, murmushi yayi sannan yaci gaba da magana "momy kwananshi ne yakare shiyasa har yahadu damu kuma ina tabbacin mutuwarsa tun kafin mujefashi a teku" [11:36PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: 21ALKAWARI Part21... Ranar talata 01-07-2014, kamar kullun yauma mutane ne cike makil acikin babbar kotun dake garin katsina, mutane dayawa sun hallara domin son jin yadda wannan shari'ah zata kasance, sbd shari'ar ta zagaya nigeria yadda mai karantawa baya tinani sbd alhaji jafar muhammad yana daya daga cikin manyan kasar nan, shiyasa wasu mutane dayawa ma ba yan garin katsina bane amman sun hallara, domin sunsan ba karamin abu bane zaisanya alhaji jafar kai kara a kotu, wasu mutanen kuma sunzo ne sbd yadda mutane ke zuzuta abin, wasu suna cewa "ankama dan mafia ya yanka dan gidan alhaji jafar zai fiddamai yan hanji sai police suka kamashi". Wasu kuma cewa sukeyi "wani dan siyasa ne abokin gaba yasa akashe dangidan alhaji jafar sbd anaso adagulamai lissafi a wannan zaben na 2014", kai maganganu dai da dama kowa da yadda yake tsara abinsa, shiyasa kotun ta dauki mutane dayawa kowa yazo domin yakashe kwalkwatar idonsa. Tacikin mutane aka ratso dani, muna shigowa kowa yamaida dubansa akaina wasu suna tabe baki, wasu kau hararata sukeyi, wasu kuma yadda naga yanayinsu da ba cikin kotu bane da har buguna sai sunyi, wasu kau fuskarsu asake hankalinsu kwance. Hakan tasa dole nasunkuyar dakaina ina tafiya ahankali har zuwa cikin wani dan akurki inda masu laifi suke tsayawa, dago kaina nayi naga dandazon mutanenda suka hallara a kotun domin ni... Cikin zuciyata nace tabbas tunda nike a duniya tsawon rayuwata bantaba ganin shekarar da tazoma mutane da rikici ba kamar 2014, itace shekarar da aka zubar da jinin miliyoyin mutane acikinta, wasu kuma suka rasa rayukansu, itace shekarar da rayuwar dan adam takoma kamar rayuwar sauro, idan ankashe mutun ankashe banza sbd babu wani matakin da ake dauka indai talaka ne, itace shekarar da aka rinka satar mutane kamar yadda mahaukaci yake tsintar leda akan titi, ni kaina nashaida 2014 sbd acikine nafada sharrin da babu wanda zai iya fiddani sai Allah, yakamata mugyara zuciyoyinmu mukoma ga Allah domin kubuta daga wannan yanayi.... Muryar maga takarda ce tayi silar dawo dani daga tinaninda nakeyi, "Yau kotu zatayi zama nabiyu acikin karar da alhaji jafar yakawo akan kisan dansa wanda ake zargin yusuf bashir da aikatawa, dafatan lauyoyin ko wane bangare sunzo da shaidun da kotu take bukata" yafada tareda zaunawa akan kujerarsa, sannan alkali yaduka yadanyi rubuce rubucensa wanda yasaba sannan yadago kansa, "idan akwai wanda yakeda magana zai iya farawa" alkali yafada yana kallon bangaren lauyoyin... Barista auwal ne yamike yazo agabana "yusuf kana yawan zuwa gidan alhaji jafar ako wane lokaci kaga dama hakane ko bahaka bane?", hakane, nabashi amsa atakaice, "inaso kotu tabani dama domin gabatar da mai gadin gidan Alhaji jafar anan" barista yafada tareda rusuna kai agaban alkali, "kotu tabaka dama" alkali yafada. Hankalinshi kwance yaratso mutane tareda zuwa yatsaya inda masu bada shaida ke tsayawa, sannan barista auwal yayi tattaki izuwa gabanshi, "malan kotu tanaso tasan ko kai waye" barista yafada yana kallon mai gadi, Sannan mai gadi yagyara tsayuwa tareda gyara zaman hularsa abisa kansa, "sunana auwalu amman ana kirana da kalafta" yafada yana duban barista, "malan kalafta ko kasan wannan?" barista auwal yafada tareda nunoni da dan yatsa, "eh nasanshi sbd yana yawan zuwa gdan alhaji, kuma ko daren ranarda za akashe aliyu, yazo gdan" kalafta mai gadi yafada yana kallona. Ji nayi gabana yafadi dass sbd akalla nakai sati guda banje gdanba, tun lokacinda yasmeen tasanarmin da zabinda mahaifinta yayimata. Barista yaci gaba da magana "malan kalafta, yusuf yaje gdan alhaji awannan ranar wane yanayi kaganshi, ina nufin daren ranarda abn yafaru?". "Tabbas ranar wurin karfe 9 na dare ina zaune a bakin kofa sai naga yusuf yashigo ranshi abace, har inamai magana amman yayi shiru bai tankamani ba, saidai yawuche yana huci kamar tukunyar dambu" kalafta yakarasa maganarsa yana kallona da wutsiyar ido. Cikin zuciyata nace lallai kalafta mai gadi kacika makiri... Bayan barista yagama yima kalafta mai gadi tambayoyi sai yajuya yayima alkali godia, sannan alkali yace "ko lauya wanda yake kare wanda ake tuhuma yanada tambaya akan mai gadi?", sai alokacin barista sady tamike akaro nafarko tayi magana "eh ya mai girma mai shari'ah" karasawa tayi a'inda kalafta yake tsaye tafara tambayarshi "malan kalafta zaka iya fadama kotu ko miye aikinka a gdn alhaji?", "eh ni mai gadi ne" yafada, "shekararka nawa kana aiki a gdn alhaji" takuma tambayarshi, "akalla nakai shekara 8" yabata amsa atakaice, sannan sady tadanyi murmushi tareda fadar "shekara takwas kana gadi alamar ka kware kenan acikin aikinka", "tabbas alhaji ma yana alfahari dani" kalafta mai gadi yafada. Sannan sady tadan karkace kai tareda fadar "a matsayinka na kwararren mai gadi wanda yadade yana aiki, ya akai lokacinda yusuf yashiga gdn alhaji cikin fushi, kakasa fadama masu gdn, ko kafadama alhaji abnda ke faruwa" sady tafada tana kallon kalafta mai gadi...... [11:36PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: ALKAWARI Part22... Barista sady taci gaba da magana "a matsayinka na kwararren mai gadi wanda yadade yana aiki, ya akai lokacinda yusuf yashiga gdn alhaji cikin fushi, kakasa fadama masu gdn ko kafadama alhaji abnda ke faruwa". Wani dan gajeren murmushi yayi kamar daman yashirya amsar tambayar da za'ayimashi, daga bisani kuma yace "Nifa aikina gadi, babu ruwana da matsalar cikin gida saidai inhana matsala shiga cikin gda, kuma nasaba ganinshi tareda marigayi aliyu" kalafta mai gadi yafada, sannan sady tajuya agun alkali tayima kotu godiya tareda komawa mazauninta. Barista auwal ne yazo wurin kalafta mai gadi yaci gaba da magana "mungode malan auwalu kalafta zaka iya komawa mazauninka", sannan barista yajuyo aguna tareda fadar "yusuf anshaida mana kaje gdn alhaji daren ranarda wannan abu zai faru acikin wani yanayi, kotu tanaso kafadamana abnda yakaika gdn a irin wannan lokacin" barista auwal yatambayeni. Hawayene kawai ke zuba a idanuwana nakasa buda baki inyi magana sbd bansan abnda zanafada ba, shirunda nayi nadan seconds 30 shine yasanya barista auwal yaci gaba da magana "idan bazaka iya bada amsa ba ni bara inbada amsar" sannan yagyara tsayuwa yaci gaba da magana "kaje gdn Alhaji da niyar aikata abnda zuciyarka tabaka amman sai kayi rashin sa'a baka samu damar aikatawa ba sbd kasamu akwai mutane acikin gidan, kaikuma baka bukatar asirinka yatonu shiyasa ka yanke shawarar tadda shi har katsina club domin cimma burinka" yana zuwa anan sai yajuyo gaban alkali yana magana "idan kotu tabani dama zangabatar da shaidata ta gaba" barista auwal yafada. Wani kasurgumin kato ne yaratso jama'a yana tafiya kamar agwa-gwa sbd kafafuwanshi kamar duk bai-bai suke, daya ta kalli gabas daya kuma ta kalli yamma, yakaraso inda akatanada domin masu shaida, bayan yatsaya sai barista yaje akusa dashi yafara magana "malan ko zaka iya sanarwa kotu ko kai waye?" barista yafada yana wani karkace kai, "sunana (Isah bare), kuma nine shugaban masu kare lafiyar mutanen gidan alhaji, (body guard)" yafada acikin wata katuwar murya. "malan isah bare ko kasan wannan?" barista auwal yafada yayinda yake nunoni da dan yatsa, "eh nataba ganinshi sau daya a airport" isah bare yafada yana girgiza kai. "a airport kuma me yahadaku ne a airport?", barista auwal yafada, saida isah bare yayi wani nishi sannan yaci gaba da magana "wata rana munje airport domin raka yasmeen diyar Alhaji zata tafi makaranta, lokacin ina tare da hajiya bilkisu wadda duk inda zataje dani take tafiya amatsayin body guard, bamukai ga shiga cikin airport dinba sai gashi yazo yana sauri zai shiga, ananne muka kamashi da makami (wuka) ajikinsa, munyi kokarin mukwace makamin kuma muji dalilin zuwansa amman yaki yadda, har yasamu hanya yagudu muma muka rufamai baya daniyar kamashi, muna cikin gudu ne wayarshi ta fadi, damukaga yayimana nisa sai muka kyaleshi muka dauki wayar (phone),Muka dawo filin jirgin domin gudun faruwar wani abu idan bamu nan" isah bare yakarasa maganarsa yana kallon barista, mungode (isah bare body guard), barista yafada, daga bisani kuma yajuyo aguna "malan yusuf inafatan kaji abnda isah bare yafada" barista yafada. Dagamai kai nayi alamar "eh", "kayarda abnda yafada gaskiya ne kenan"barista yafada. Wlh ba gaskiya bane, nakarasa magana cikin kuka. murmushi kawai barista yayi sannan yafiddo wata waya daga aljihunsa "kasan wannan wayar?" barista yatambayeni. Tabbas nayi mamaki matuka, sbd wayata ce nagani wadda tabace tun lokacinda aunty bilki tasa akaman bugun tsiya a airport. Dakyar na iya bude baki nabashi amsa, eh wayata ce. Sannan barista yamikama maga takarda shikuma maga takarda yamika ma alkali, alkali yana dubawa. Sannan muryar barista auwal taci gaba da tashi "ina fatan kotu zata fahimci rashin gaskiya atareda wanda ake tuhuma sbd yakaryata gaskiya domin neman kubutar dakanshi, wannan itace wayarshi wadda tafadi lokacinda yake neman kubutar dakanshi ahannun su Isah bare body guard. Kuma inaso kotu tasan yusuf ya dade da alwashin kashe wasu daga cikin iyalan alhaji sai yanzu Allah yabashi sa'a"... "Idan dayan bangaren sunada magana akan maganar da akayi yanzu zasu iya gabatarwa" alkali yafada, sannan barista sady tazo agaban isah bare, tafara magana "isah bodyguard kotu tanaso ka maimaita maganarda kafada yanzu, abnd yafaru a airport...", shiru isa body guard yayi har tsawon second biyar, daga can gefe naji muryar barista auwal tana tashi "Objection ya mai girma mai shari'a yakamata kotu tasanarda mai tambaya nan ba wurin wasa bane da har za arinka magana ana maimaitawa" barista auwal na rufe baki sai sady tadauka, "yakamata kotu tayi watsi da wannan korafi sbd anaso wannan kotu mai adalci tagano gaskiyar abnda ke faruwa, idan abnda yafada gaskiya ne, to zai iya maimaitawa batareda kuskure ba", "korafi bai karbuba" alkali yafada... Sannan sady tayi godia, isah bare yafara magana kamar zai iya maimaitawa dai dai, kuma kamar bazai iyaba.... [11:57PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: 23ALKAWARI Part23... "yakamata kotu tayi watsi da wannan korafi sbd anaso wannan kotu mai adalci tagano gaskiyar abnda ke faruwa, idan abnda yafada gaskiya ne, to zai iya maimaitawa batareda kuskure ba", "korafi bai karbuba" alkali yafada... Sannan sady tayi godiya ga alkali tajuya wurin isah bare tareda bashi iznin yamai maita maganar daya fada, kallo daya zakamai kasan yana cikin fargaba, sunkuyar dakai yayi yafara magana kamar zai iya maimaitawa dai dai, kuma kamar bazai iyaba. Nayi mamaki matuka ganin yadda yasaki jikinshi yaci gaba da magana hankalinshi kwance kamar wanda yabuda littafi yana karantawa, saida yamai maita kalamansa kaf batareda yayi kuskure ba, sannan yadaga kanshi suka hada ido da barista auwal naga sunyi wani murmushi gaba dayansu, cikin raina nace, lallai wannan al'amari akwai lauje acikin nadi, barista sady kau dake tsaye agaban isah bare kasa motsawa tayi tana kallonsa kamar tana shirin yimai wata tambayar amman sai naga tajuya cikin damuwa tayima alkali godiya takoma wurin zamanta. Tasowa barista auwal yayi agaban kotu tareda fadar "idan wannan kotu mai adalci ta bani dama zan gabatar da wani jami'in tsaro wanda yasan wani abu daga cikin wannan case din", "kotu tabaka dama", alkali yafada yana daga kansa. barista yakarasa maganarsa yana kallon inda mutane suke zaune burjat suna kallon wannan birkitacciyar shari'ah. Ratsowa yayi cikin mutane sanye da bakaken kayanshi na ma'aikata bai zame ko ina ba sai agaban barista auwal, sannan barista yayimai nuni da wurinda masu bada sheda ke tsayawa tareda fadar "bismillah sajen", kallo daya nayimai naganeshi, shine mutun nafarko da yayi silar shigowata nan wurin, sbd shine mutun nafarko dayafara rikeni dasunan mai laifi hadda sanyaman ankwa... Tsaye yake yamaida hannuwansa abaya ko motsawa bayayi saidai kallon mutane dayakeyi daya bayan daya, sannan barista yazo gabanshi yatsaya "kotu tanaso tasan ko kai waye" barista yakarasa maganarshi yana duban sajen, "suna na sajen lawal gwanda kuma ni jami'in tsarone ina aiki a karkashin sabon gari station" lawal gwanda yafada, sannan barista yagyara tsayuwarsa yaci gaba da magana "sajen lawal gwanda ko kasan wani abu dangane da kisan da akayiwa dan gidan Alhaji jafar muhammad?" barista yakarasa maganarsa tareda dan kannare idonsa guda da alamar tambaya karara a fuskarsa, gyaran murya sajen lawal gwanda yayi sannan yafara magana "tabbas ina daya daga cikin jami'an tsaronda suka kama wannan mai laifin. Ranar talata 3-6-2014 Muna cikin aiki sai mukaga wata mota tawuce a cikin gudu wanda yawuce ka'ida, munyi kokarin mutsaida mai tukin amma yaki tsayawa, dole saida muka bishi amman yasamu sa'a yabace mana tundaga roundabout din kofar kaura, dukda haka bamuyi kasa a gwuiwa ba mukabi hanya ko munganshi, harsaida mukaje katsina club inda ananne muna dai-dai zuwa muka taradda wannan bawan Allah yadurkusa da mutun agabansa sai dakamai wuka yakeyi aciki, munyi iya kokarinmu wurin ganin munyi sauri mun isa a'inda suke amman kafin mukarasa har yagama aikinsa" Sajen lawal gwanda na zuwa nan da zanjensa sai yafashe dawani irin kuka wanda yakarya zuciyar musu saurarenshi, daga bisani kuma yaci gaba da magana "na dade ina aikin dan sanda, kuma na kama masu laifi dayawa, amman bantaba ganin case dinda yatadaman hankali ba kamar wannan, yadda naga yaduka yana dakama dan tahalikin Allannan wuka aciki babu alamar imani atare dashi balle ayi maganar tausayi, bai daina dakamai wukaba har saida muka...." yana zuwa nan sai yayi shiru alamar kuka ne yaci karfinsa har yakasa ida maganarsa. Nan take wasu gunguni kasa kasa suka rinka tashi acikin kotun, masu sallallami nayi masu tsinuwa nayi, hadda masu yin Allah ya isa. Nikau wani abune naji yataso ya tokareman makoshi shi baikoma ciki ba shikuma bai fito ba, sai alokacin na hango umma zaune takuraman ido sai faman zubarda hawaye take kusa da ita hadiza ce ta hada kai da kujera, ko baka tambaya ba kasan kuka takeyi... Saida alkali yabuga wata guduma akan teburinsa sannan kotun tayi tsit kamar babu kowa aciki. Barista auwal yadafa kafadar sajen tareda6 fadar "kayi hakuri sajen kunyi iya aikinku kuma, za'ayi ma wannan mai laifi hukunci dai dai da laifin daya aikata, mungode sajen zaka iya tafiya" yana gama magana da sajen kuma sai yajuya agun alkali "ina fatan kotu zatayi duba zuwa ga wa'annan kwararan hujjojin dasuka gabata domin yin amfani dasu wurin zartar da hukunci akan wanda ya aikata wannan laifin yadda masu hali irin nasa zasu gani suma sudaina" sannan yayi godiya ga alkali yakoma yazauna kusa da barista sady wadda fuskarta tacanza kamar wadda aka aikomawa da rasuwar iyayenta. "ayau 1-7-2014 ne kotu takawo karshen wannan shari'ah bayan sauraren kwararan hujjoji da kotu tayi....." turo kofa da akayi dakarfi, shine yayi silar tsaida alkali daga maganar dayakeyi... "ku dakata" naji amfada da karfi. cikin hanzari tanufo alkali da wani mutun a bayanta da alama da gudu suka karaso kotun yadda naga su dukansu sunata faman sheshsheka...... [11:57PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: ALKAWARI Part24..... "ayau 1-7-2014 ne kotu takawo karshen wannan shari'ah bayan sauraren kwararan hujjoji da kotu tayi da....." turo kofa da akayi dakarfi, shine yayi silar tsaida alkali daga maganar dayakeyi... "ku dakata" naji amfada da karfi. cikin hanzari tanufo alkali da wani mutun a bayanta da alama da gudu suka karaso kotun yadda naga su dukansu sunata faman sheshsheka... Nayi mamakin ganin haleematu cikin kotu a irin wannan lokacin, wasu tambayoyi ne suka rinka ziyarta kwakwalwata, me yakawota? Ya akai tasanda wannan al'amarin? Saidai bansan amsar tambaya ko daya daga cikiba. "wlh bashi yakashe shi ba" takuma fada a karo na biyu, wasu yan sanda ne guda biyu sukayo kansu da niyar fiddasu daga cikin kotun, ga mamakina sai naga alkali ya daga masu hannu alamar su tsaya, yan sandan nan basuyi gardama ba wurin bin umarnin alkali ta hanyar komawa inda suka fito. Kotun tayi tsit kowa hankalinshi yakoma agaban alkali domin ganin abnda ke faruwa "maimaita abinda kika fada" alkali yafada yana kallonta "wallahi wanda ake zargi bashi ya aikata wannan laifinba" cikin wata murya kamar wadda take shirin yin kuka. alkali yakuma dubanda tareda tambayarta "ke wacece?", "suna na haleematu usman zango" tabashi amsa atakaice, alokacin alkali ya ajiye alkalamin dake hannunsa ya harde hannuwanshi guda biyu yakara jefomata wata tambayar, idanuwanshi akanta ko kiftawa bayayi, "Haleematu kinada shaida akan abnda kika fada?" tunkafin yarufe bakinshi ta dagamai kai alamar "eh" sannan kuma tafada a bayyane "eh" tareda juyowa bayanta tanuna wannan mutumen wanda suka shigo tare kansa a duke. Alkali yadubesu sannan yadauki alkalamin dake a gabansa yayi rubuce-rubucen da yasaba, sannan yadago kansa yaba mutumen umarnin yashiga inda aka tanada domin bayarda shaida, batareda bata lokaciba yakarkata akalarshi yashige cikin dan akurkin da masu shaida ke tsayawa... Cikin hanzari barista sady tamike tayi tattaki zuwa inda yake tsaye, "bawan Allah kotu tana bukatar sanin ko kai waye" barista ta tambaya, "sunana idi mai gadi" yabata amsa atakaice, sady ta daga kanta tadubeshi tace "idi mai gadi, kamar yadda kotu take zato kasan wanda yayi wannan kisan, ya abin yake?" sady tafada da alamar tambaya a fuskarta, sannan idi mai gadi ya girgiza kai kamar kadangare tareda cewa "eh tabbas naga wa'anda sukayi wannan kisan", "kotu tanason taji gaskiyar abnda kasani" barista sady tafada tareda kurawa idi ido, "ranar wata talata ina cikin dan dakina wanda aka tanada domin masu gadi, ina zaune ina sauraren radio sai naji kamar ana kokowa, sai banmaida hankali akai ba saboda nasan wurine na mutane, jim kadan kuma naji ankwalla wata irin kara wadda dukwanda yaji karar yasan bata lafiya bace, hakan yasa nafito domin inga abinda ke faruwa, ina fitowa nagansu tsaitsaye sun rufe fuskarsu da wani bakin abu, ga wani dan saurayi wani dan saurayi kwance a gabansu da wuka soke a cikinsa sai jini ke bin jikinsa, nayi yunkurin inruga domin neman ceto agun mutane amman nakasa ko juyawa Nakasa motsawa daga inda nike, nan take nayi mutuwar tsaye, na kasa buda baki inyi magana balle mutane suji, har sukagama abnda sukeyi suka juyo domin tafiya sai suka hada ido biyu dani, nayi zaton zasu tafi su kyaleni amman naga sunyo kaina sun sungume ni suka sanya acikin mota suka kaini bayan gari, daya daga cikinsu yace akasheni kawai saboda kar asirinsu yatonu, sai wani yace a'a kar sukasheni da hannunsu amman suyiman abinda zanmutu dakaina bayan nasha wahala, nanfa suka hau duka na saida sukaga ko dan yatsa bani iya motsawa sannan suka daukeni zasu jefa acikin ruwa, sai daya daga cikinsu ya daureman ido dawani kyalle daganan bansan abnda yakara faruwa ba saidai nabude ido naganni cikin asibiti wannan baiwar Allah tana dubani, wadda itace ta ceci rayuwata" yakarasa maganarsa yana nuna haleematu, sannan barista sady tace "lallai idi mai gadi kasha wahala" lokacin tayi wani nishi mai kama da ajiyar zuciya, daga bisani kuma taci gaba da magana "yanzu idan kaga wa anda sukayimaka wannan ta'annadin zaka iya ganesu?", "eh zangane su indai naga fuskar daya daga cikinsu" inji idi mai gadi, "idi mai gadi akwai daya daga cikin mutanen dake zaune anan?" takarasa maganarta tana nuni da mutanen dake zazzaune suna kallon wannan shari'ah marar kan gado. Nanfa idi mai gadi yafara duban mutanen dake zazzaune a kotun kowa yasha jinin jikinshi... Cikin hanzari barista auwal yamike tareda fadar "Objection ya mai...." tunkafin yakarasa maganarsa Alkali yatarbi hanzarinshi da cewa "korafi bai karbu ba"............. [11:57PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: 25ALKAWARI Part25.... Cikin hanzari barista auwal yamike tareda fadar "Objection ya mai..." tunkafin yakarasa maganarsa Alkali yatarbi hanzarinshi da cewa "korafi bai karbu ba", barista auwal yakoma yazauna a sanyaye, barista sady kau wani dan gajeran murmushi kawai tayi tareda ba idi mai gadi umarnin yaduba acikin mutanen ko za'aga daya daga cikin wa'anda ake nema. Cikin lokaci dan kankane kotun tayi tsit ko kwakwkwaran motsi babu maiyi, saidai wannan yakalli wannan, wannan yakalli wancan, nan take wani zafi yayoma kotun lale marhabin dukwanda kagani sai zufa (jibi) yakeyi kamar wa anda aka watsama ruwa. Cikin raina nace wai abinda nake ganin yana faruwa acikin wasu fina finai da littattafan marubuta, shine yau yake faruwa agabana kuma akaina... "Ga daya chan!!!" kalmar datayi silar maidoni daga tinanin danakeyi, itace kalmar data tada hankalin dukwanda yake acikin kotun, ni kaina saida gabana yafadi sanadiyar jin wannan kalma, "ga daya can zaune" idi mai gadi yakuma fada a karo nabiyu yana nuna gungun wasu mutane dake zaune acan baya. Tunda nike tsaye a kotun bantaba sanin suna nanba sai yanzu... Abba ne zaune akan kujera daga gefenshi kuma mahaifiyarshi ce aunty bilki, daga bayansu kuma wasu bakaken mutane ne tsai tsaiye kamar gumaka. mikewa yayi kamar wanda aka tsira ma allura "karya yakeyi kada ku saurareshi" abba yafada a rikice bakinsa har wani kumfa kumfa yakeyi, kafin yakara motsawa yaji wasu police guda biyu sunyi carab da kugunshi suka jawoshi har agaban kotu. Barista sady takalli idi mai gadi tareda cewa "ka tabbata yana daga cikinsu?" ta idar da maganarta tana nuna abba amman idanuwanta suna akan idi mai gadi. "eh shine, bazantaba manta wannan fukar ba" idi yafada yana nuna Abba. "mungode idi zaka iya zuwa kazauna, mai yiyuwa zamu bukaci wani abu agareka nan gaba kadan" barista sady ta fadama idi.. "Ya mai shari'a inaso abani dama domin zantawa da abokiyar tafiyar idi mai gadi" sady tafada tana duban alkali, "kotu ta amince" alkali yabata amsa atakaice, batareda bata lokaciba haleematu ta hallara agaban kotu, "malama kibayyana ma kotu ko ke wacece", "sunana haleematu usman zango, kuma ni likita ce mai zaman kanta a asibitin a Alheri clinic a garin zangon daura", barista sady tadan nisa sannan takuma tambayar haleema, "malama haleematu, ko ince doctor haleemah, tabbas aikinki yayi rana kuma yayi amfani ta hanyar ceton rai biyu lokaci guda, amman kotu tanaso kifadi abnda kika sani, dakuma yadda har kukasan da wannan shari'ah?" sady takarasa maganarta tana duban haleemah, "ranar wata talata da misalin karfe 8:30pm, wasu makiyaya suka kawomana marar lafiya magashiyan, bamuyi niyar amsarsaba saboda 9:00pm muke tashi, amman ganin yadda marar lafiyar yake yasa dole muka amsa saboda zai iya rasa ransa akowane lokaci. Hannunsa daure fuskarsa ma daure dawani hankici, haka suka kawoshi kuma suka shaida mana cewa abakin ruwa suka sameshi, suma basusan abnda yafaru dashiba, anan asibitin muka dauki dawainiyarshi tundaga aikinda akayimai, har kudaden magani hartsawon wata guda sannan muka samu yaji sauki sosai har yake iya takawa yana tafiya dakanshi, sannan yabamu labarinshi da abnda yafaru dashi, kamar yadda yafadamaku abaya" haleematu tana zuwa nan da zancenta sai tayi shiru, itakuma barista sady dataga haka sai takara jefomata wata tambayar "ya akai kukasan wannan shari'ar ta shafi abnda akayima idi mai gadi?" sady tafada fuskarta cike da mamaki, haleematu kau gyara tsayuwa tayi taci gaba da koro bayani "wannan shari'ar tayi suna sosai acikin jahar nan harda ma kewaye, shari'ar ta zagaya ko ina ta hanyar kafafen yada labarai, kusan ko wane media sun sanarda faruwar wannan abu.. Jiya da misalin karfe 8:00pm muna zaune hadda idi mai gadi muna kallon kttv, anan mukaji sanarwar wannan shari'ah, idi mai gadi ya tabbatar mana akan wannan abn ne akayi niyar halakashi sbd dan jaridar dayayi sanarwar, saida yafadi ranar da akayi kisan kuma da wurin da abn yafaru, hakan yasa muka tabbatar da labarin da idi mai gadi yafadamamu, shiyasa muka garzayo domin fadar gaskiyar abnda yafaru", barista sady tayi ajiyar zuciya tareda girgiza kai "idan hankicin da aka daurema idi mai gadi fuska dashi yana kusa, kotu tana bukatar ganinshi", nandanan tafiddo hankicin tareda mikawa barista sady kamar daman jira take atamabayeta, barista sady taduba sannan tajuya agun alkali, "ya mai shari'ah wannan shaidar kadai ta isa ta wanke wannan bawan Allah da ake zargi, kuma wannan shaidar ta isa takama wanda ya aikata wannan laifin yakoma gefe yazauna cikin yan baruwana, yanayima mutane kallon tom and jerry, saboda ajikin hankicin harda sunanshi kuma sunan ba irin wanda ake rubutawa ba da biro ko makker, wannan daga company ne kamar yadda wasu mutanen suke zuwa anayomasu abu da sunansu ajiki", barista sady tamikama maga takarda hankici, shikuma maga takarda yamikama alkali, alkali yayi yan dube dubenshi tareda rubutun da yasaba........ [11:57PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: 26ALKAWARI Part26... Barista sady tamikama maga takarda hankici, shikuma maga takarda yamikama alkali, alkali yayi yan dube dubenshi tareda rubutun da yasaba daga bisani kuma yadago kansa yaci gaba da magana "anan kotu zata diga aya tahanyar yin amfani da kwararan hujjojin da suka gabata domin yanke hukunci, kotu ta wanke wanda ake zargi da aikata laifin kisa, kuma kotu ta yankema wanda yayi wannan aikin hukuncin zama a gdan kaso tsawon shekara 25 tareda aiki mai tsanani" Alkali yana rufe bakinshi yabuga gudumar dake ajiye agefensa tareda mikewa tsaye. Batareda bata lokaci ba wasu police suka sanyama abba ankwa suka fice daga kotun... Nan danan naga mutane sunyo kaina sai mikoman hannu sukeyi daniyar mugaisa, wasu nayiman barka wasuma bansan abnda suke cewa ba sbd hankalina yana agun umma na wadda take tsaye ta daga hannayenta sama tanayima Allah godiya... daganan bamutsaya wani abuba muka dunguma muduka zuwa gida....... Nida umma mun nuna farin cikinmu sosai tareda nuna jin dadinmu akan namijin kokarin da haleematu da barista sady sukayi mana. Bayan sati daya dagama wannan shari'ah muna zaune nida umma da hadiza muna fira, kamar yadda muka saba sai mukaji anyi sallama, dukda banjuya ba amman nagane muryar wanda yayi sallamar, usman ne yashigo har gaban umma yazauna yagaisheta fuskarshi da alamar damuwa "umma kiyi hakuri da duk abnda yafaru kuma ina rokonki gafara kiyafema mahaifinmu akan abinda yafaru tabbas yayine akan rashin sani..." kafin yakarasa maganarsa umma tadagamai hannu "ya isa haka, babu abnda kukamana kuma, kuje Allah yasanyamaku Albarka, idan kuma mahaifinnaka ne ya aiko ka, kacemai babu komai" umma tafada cikin wani yanayi fuskarta babu yabo kuma babu fallasa, nayi zaton usman zaiji dadin maganarda umma tafada amman sai naga fuskarshi bata canja ba daga alamar damuwar dake damunshi, "ai yanzuma tareda alhaji mukazo shi yace inkawoshi" usman yafada lokacinda yasunkuyar dakanshi kasa yana wasa da makullan dake hannunshi, "da ba kai kadai kazo ba, amman kabaroshi waje yanata jiranka kamar wani abokinka" cikin sigar fada take maganar, "tashi mana, yusuf kuje kushigo dashi" takarasa maganarta tana kallona... Tunkafin mushigo hadizah ta shimfida tabarma yadda kowane bako yagani yasan shi akayima wannan shimfidar, shiyasa alhaji baiyi wata wata ba kawai yazauna akan tabarmai, bayan sungama gaisawa ne alhaji yake fadama umma "nazo dakaina ne domin abnda yafaru lokacin baya, tabbas kuskure ne anriga anyi kuma ina rokonku kuyafemana, bawai dan matsayina ba ko dukiyata ba, shiyasa nataso dakaina batareda na aiko wani ba", "a'a babu komai alhaji wannan abu matsayin kaddara ne ko ince kaddara ce daga Allah, shikadai yasan dalilinda yasa haka tafaru atsakaninmu, bakada laifi alhaji ai danda mutum yahaifa kuma aka kaudashi alokaci guda ai dole mutun yadau mataki tare da bin diddikin abnda yafaru, wannan shine halin iyaye nagari masu kula da yaransu, babu komai wlh komai yawuce" umma takarasa maganarta tana girgiza kai amman idanuwanta suna kallon kasa "Nagode sosai" alhaji yafada atakaice, sannan kuma yaci gaba da magana "kuma naji duk abnda ke tsakanin yaron wajenki da diyata... Kinsan aure wani nauyi ne wanda mutun zai dauka kuma aure bazaitaba yiyuwa ba idan babu sana'a, hakan dana fada bawai yana nufin na hanashi auren diyata bane, amman gaskiya bazan bayarda itaba a'inda zatasha wahala, kuma bazan iya sakin akuya ba daga baya tadawo tana ciman danga, su yara ne bazasu iya fahimta taba, amman ke amatsayinki na babba kuma mahaifiyarshi kinsan abnda nike nufi". "haka Allah yaso alhaji ai duk abnda Allah yaso to babu yadda bawa zayayi, talauci da dukiya dai duka na Allah ne, Allah yasa hakan shi yafi alkhairi" umma tafada. Ba karamin faduwa naji gabana yayi ba sanadiyar jin wa'annan maganganun da alhaji ke fada, ina dago kaina sai nahangi usman hawaye sai tsiyaya suke daga fuskarshi, cikin raina nace daman yasan za'a hanani auren yasmeen ne shiyasa yazo ranshi abace, a gurguje alhaji ya ida maganarsa wanda ni banma san abnda yake fada ba sbd hankalina gaba daya yabar jikina, "to sai anjima Allah yakiyaye" naji umma tafada sai lokacin nalura alhaji da usman har sun miike tsaye suna niyar tafiya, nikuma danaga haka sai nayi sauri namike tareda mikama usman hannu daniyar mugaisa tunda zasu tafi, ga mamaki na sai naga Alhaji yamikoman hannu shima muka gaisa, mungaisa lafiya lau amman abnda yabani mamaki shine, alhaji yakurama hannu na ido, kuma nakasa gane abnda yake kallo, nayi kokarin fidda hannuna daga cikin nashi hannun amman naji yakara rikewa gam, kamar anyimai umarni da yarikeni kar ingudu, nakara duba hannu na naga babu komai ajiki inba zoben dake acikin danyatsa na ba...... [11:57PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: 27ALKAWARI Part27.... Zaune suke acikin falo babu maiyima wani magana acikinsu, kowa hankalinshi a tashe kamar yan zaman gaisuwa... Usman da yasmeen ne suke zaune akan carpet dinda ya mamaye falon sun sunkuyar dakansu kasa, daga chan gefensu kuma aunty bilky ce zaune. Akan kujera kuwa mahaifiyar su yasmeen ce tare da mijinta alhaji jafar, wanda yahada hannayenshi guda biyu yadora abisa kanshi yana kallon kasa kamar mai shirin kwalla ihu, sunkai wurin dakika 2 babu wanda yayi magana acikinsu, alhaji ne yadago kansa fuskarshi cike da damuwa, yakalli yaranshi guda biyu dake zaune usman da yasmeen sannan yamaida dubanshi ga kanwarsa aunty bilky mahaifiyar abba, sai alokacin alhaji yakatse shirunda yamaida dakin kamar makabarta "na kulle ku har tsawon wani lokaci sbd ina tinanin zaku kawoman matsala acikin wannan shar'iah wadda aka kashe dan uwanku" alhaji yafada yana kallon usman da yasmeen dake zaune babu wanda yadago kansa acikinsu balle yafadi wata magana, "kuyi hakuri 'ya'ya na nayi hakane sbd naga kuna neman kukawo man matsala kuma sanin kanku ne, yazamar mani dole inga bayan dukwanda yakasheman dan danahaifa da cikina, shiyasa nadamka wannan case din a hannun kotu dan abimamu hakkinmu, matsalar dake dakwai yanzu akalar shari'ar tacanza alkibla tana neman tadawo cikin gidannan gaba dayanta, sbd abba ne mutun nabiyu wanda ake zargi kuma binciken da kotu tayi kamar yana nuna cewa yusuf da ake zargi bashine yayi kisanba" yana zuwa nan da zancensa aunty bilky tamike cikin bacin rai "haba alhaji wace magana kake son kafada ne, dukda bakai ka haifi abba ba ai abba danka ne, saboda ni nahaifeshi da cikina, kuma 'ya'yana naka ne saboda kana uwana, ta yaya kake tinanin abba zai kashe aliyu haba alhaji" takarasa maganarta tareda mikewa tsaye kamar wadda take shirin yin dambe, ganin haka ne yasa usman mikewa tsaye daniyar fita daga falon sbd bayason jin maganganun dake shiga tsakanin mahaifinshi da aunty bilky, muryar alhaji ce tasaidashi daga niyar ficewa dayake "ina zakaje?", shiru usman yayi tsawon daqiqa 5 sannan yace "dady zanje kitchen insamu abnci yunwa nakeji", "dawo kazauna, kayi waya yanzu akawo maka anan kaci" badan usman yanaso ba dole tasa yazauna, yakira kuku yafada masa uzurinsa. "ke samu wuri kizauna", alhaji yafadama bilki cikin tsawatarwa, "zama?! A ina zan zauna ana neman sanyamana kisa..." "ke ni kike fadama wannan maganar?, matsala ce wannan tataso kuma mu zamu maganceta amman kina nunaman ke dabba ce", "ni kake cewa dabba alhaji?, ni kake wulakantawa acikin 'ya'yanka gaban matarka!" bata jira komaiba ta fizgi dan kwalinta tayi waje tana sabbatu wanda babu mai iya gane abnda take fada, afusace tafita tana zuwa dai dai kan kwana indo tafadi agabanta da kwanonin abnci ahannunta, "ke mahaukaciyar inace tsohuwar banza, ni zaki fadomawa?" aunty bilki tafada tana dafe kirji, "yi hakuri hajiya wallahi tuntube nayi kuma bansan zaki karyo kwana ba kingani abincin dazankaima usmanu ne nadauko cikin hanzari ki gafarceni" indo tafada cikin sanyin murya, ko saurarenta bata tsaya yiba, tawuce fuuu....... Saura kwana biyu akoma kotu wanda ake tinanin shine zama na karshe a cikin wannan shari'a wadda tashare watanni ana gabatarwa... Umma ce zaune tareda hadizah kanwata, dakuma haleematu (doctor). Zaune suke suna tattaunawa akan wannan shari'ah su dukansu suna jimamin sakamakon dazai wakana bayan angama wannan shari'ah. "umma zantafi gida kafin yamma tayi zanbiya wani wuri ne" haleematu tafada tareda sanya hannu daniyar daukar jakarta, "to tunyanzu, bakibari ko rana tayi sanyi", "aa umma kinsan hanyar tamu batada kyau, kuma inaso zanbiya gdan wani kanin baba na shiyasa", "to diyarnan mungode Allah yakaiki gda lafia, kigaidaman mahaifan naki" "ameen umma zasuji", hadizah tarakata har bakin motar ta... bayan tafiyar haleematu baifi 30mnt ba sai ga barista sady tashigo, ba karamin dadi umma tajiba data ganta sbd itace lauyar datake kare ni batareda ankirata ba kuma batareda anbiyata ba.. Agajiye tashigo tanemi wuri tazauna. Hadizah ta tashi ta debomata ruwa... "umma mun gama duk bincikenda yakamata muyi yanzu rana kawai muke jira tazo, kuma kitayamu da addu'a Allah yabamu sa'a" sady tafada lokacinda take ajiye cup dinda ke hannunta, "addu'a itace muketayi koda yaushe barista, mungode da irin wannan halacci dakike nuna mana", "a'a umma babu komai wannan kamar nayima kaina ne" sady tafada, "samun irin haka yanzu yanada wahala, musamman ma ace mutun bai sankaba kuma bakasanshi hakanan yashigo rayuwarka yataimaka maka ai ya cancanci yabo..." Umma kibar wannan maganai, yanzu zanje gdan alhaji jafar wurin usman abokin yusuf, akwai wasu bayanai danike bukata agunshi, gashi kuma lokaci yakure, saura kwana biyu akoma kotu", sannan tamike tsaye tana magana "daman zuwa kawai nayi ingaidaku kuma insanar daku cewa mungama komai" barista sady tafada, "mungode sosai Allah yashigarmana gaba, kuma Allah yabada sa'a" inji umma........ [11:57PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: 28ALKAWARI Part28.... kamar kullun yauma kotun tacika makil da mutane amman da alama yau mutanen sunfi yawa saboda har ta window kawunan mutane ne suke lekowa, wa anda basu samu wurin zama acikin kotun ba... "ayau kotu zataci gaba da sauraren kara wadda Alhaji jafar muhammad yashigar akan kisan gillar da akayima dansa Aliyu, wanda ake zargin mutun biyu wa anda ke tsare da aikata laifin, yusuf da Abba kuma wannan itace shari a tafarko daza afara gabatarwa a safiyar yau litanin wadda tayi dai dai da 11-8-2014" maga takarda yana kammala bayaninsa yasamu wuri yazauna, adai dai lokacin aka shigo damu kowannenmu daddaure kamar awaki. Wuri daya aka hadamu nida abba acikin wani dan akurki muna fuskantar mutanenda sukayima kotun cikar kwari.... Alkali yakalli bangaren da lauyoyin suke zaune barista sady ce tafara mikewa, cikin kayan aikinta "kamar yadda kuka sani nice barista sady kuma nice lauya wadda take kare wanda ake zargi na farko (yusuf)" tana gama fadar haka tayima alkali godia tareda zama wurinta.... "sunana barista auwal kamar yadda akasani, kuma nine nadawo amatsayin lauya wanda yake kare mutun na biyu wanda ake zargi (abba)" sannan shima yakoma wurin zamansa tareda yima alkali godia, bayan alkali yagama yan rubutunsa yakuma dago kai akaro nabiyu, "kamar yadda yagabata muna bukatar lauyoyin kowane bangare sukawomana shaidu da hujjojin da zasu gamsar da kotu akan wannan zargi da akeyima wa annan mutane guda biyu, kotu tabada dama wanda yakeda magana zai iya farawa" alkali yakammala maganarsa yana kallon inda lauyoyin suke azaune, barista auwal ne yafara mikewa "kamar yadda nafadama kotu abaya cewar yusuf shine yayi wannan kisan hakan yasa nadawoma kotu da hujjoji kwarara wa anda suke bayyana hakan, inaso kotu tabani dama domin zantawa da wa anda ake zargi" barista auwal yafada yana kallon alkali "anbaka dama" alkali yafada atakaice, barista yafara da abba "malan abba inaso kasanarma da kotu ko kai waye dakuma yadda kuke da alhaji da yan gdansa", "sunana abba ibrahim sabo, alhaji kawuna ne, kuma shine matsayin ubana, sbd tunda nabude ido a gdanshi na tsinci kaina kuma yanamin duk abnda uba yadace yayima dansa ci da sha sutura harda karatuna", "mungode malan abba" barista auwal yafada, sannan yajuya agun alkali "ya mai shari'ah inaso kotu taduba tagani tsakanin alhaji jafar dakuma abba. Ai ko kare idan akayimai wannan halaccin bazaiyi abnda ake neman cewa abba yayi ba, wannan sharri ne kawai aka lakafa masa" barista auwal yafada yana nuna abba da hannunsa amman idanuwansa suna akan alkali, "ya mai shari'ah inaso kotu tabani dama domin zantawa da wanda ake zargi na farko" barista auwal yakuma fada, "kotu tabaka dama" alkali yafada lokacinda yake rubutu akan takardar dake agabansa...Barista auwal yakaraso agabana yatsaya yana kallona daga bisani kuma yace, "basai na tambayeka kokai waye ba sbd kotu tasanka sanadiyar laifinda ka aikatane yataramu anan...". "Objection ya mai shari'ah!" sady tafada dakarfi tareda mikewa tsaye sannan taci gaba da magana, "yakamata mai magana yasan irin kalaman da zai rinka amfani dasu wurin tuhumar mutun, kuma yadaina alakantashi da laifinda ake zargi, sbd haryanzu ba'a tabbatar da wanda yayi laifinba cikin bincike ake", sady tafada tana kallon alkali, "mai magana yagyara harshensa" alkali yafada. Sannan barista sady tadan sunkuyar dakanta tayi godiya tareda komawa mazauninta... "yusuf inaso kasanar da kotu hakikanin gaskiyar yadda akayi har kasamu hanyar yin mu'amala da iyalan gidan alhaji jafar" barista auwal yafada yana kallona "mutunci ne kawai yahadani dasu" nabashi amsa, "mutunci kamar ya kenan, wa kasani acikin gidan?" yakuma tambayata akaro nabiyu, "inada aboki a gdan sunanshi usman" nafada batareda wani fargaba ba, sannan barista yagyara tsayuwarshi "minene tsakaninka da yasmeen yar gdan alhaji jafar?" nayi mamakin jin wannan tambayar hakan yayi silar daureman kai narasa abnda zancemasa, ganin haka shikuma yaci gaba da magana "idan ka kasa fada, ni bara infadamaka" barista yafada yana kallona tareda wani murmushi "yusuf kundade tareda yasmeen yanayin shakuwarku ne yasanya har soyayya tashiga tsakaninku. hakane ko bahaka bane?", kawai dagamai kai nayi alamar "eh hakane", "bayan tadawo daga makaranta kaji labarin anyimata miji, ma'ana anzabamata wanda zata aura. na fada dai dai?" barista auwal yakuma tambayata a karo nabiyu, wannan lokacinma kai kawai nadagamai kamar kadangare tareda fadar "eh hakane", sannan barista auwal yajuya agun alkali yaci gaba da magana, "ina fatan kotu zatayi duba kuma tayi la'akari da irin abnda yashiga tsakanin iyalan gidan alhaji jafar da yusuf, kowa yasan zafi dakuma radadin da masoya keji idan aka rabasu da junansu, wannan kadai ya isa gaba tashiga zuciyar yusuf shida yan gidan su yasmeen, har zuciyarshi tasa ya aikata mummunan aiki akansu da niyar daukar fansar abnda akayimai. sai tsautsayi ya afka akan marigayi aliyu... [11:57PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: ALKAWARI Part29.... Barista auwal yajuya agun alkali yaci gaba da magana, "ina fatan kotu zatayi duba kuma tayi la'akari da irin abnda yashiga tsakanin iyalan gidan alhaji jafar da yusuf, kowa yasan zafi dakuma radadin da masoya keji idan aka rabasu da junansu, wannan kadai ya isa gaba tashiga zuciyar yusuf shida yan gidan su yasmeen, har zuciyarshi tasa ya aikata mummunan aiki akansu da niyar daukar fansar abnda akayimai. Kuma ya mai shari'a na tanadi shaidu wa anda suke nuna cewa ba abba bane yayi wannan kinsanba, inaso kotu tabani dama domin gabatar da wa'annan shaidu nawa", "kotu tana jiran shaidunka" alkali yafada yana kallon barista auwal... Barista yamaida dubansa ga zuwa mutanen da ke zaune a kotun tareda fadar "kotu tana bukatar ganin dan tashe", batareda bata lokaci ba wanda ake nema yabayyana agaban kotu, "bawan Allah kotu tanaso kabaiyana mata ko kai waye" barista yafada, "suna na S.D dan tashe" mai bada sheda yaba barista amsa atakaice, "s.d dan tashe ya kake da abba kokuma ince me kasani akan abba" barista yafada yana kallon dan tashe, "nasan abba sosai, sbd abokina ne na kusa da kusa kuma tunda nike dashi bantaba ganin yayi wani mugun hali ba dahar za'a iya kwatantawa da kisan kai, abba ko dan tsako bazai iya kashewa ba balle mutun", "mungode sd dan tashe" barista yafada tareda komawa mazauninsa. Alkali yadukar dakansa yayi rubutu akan takardar dake gabansa sannan yadago kansa tareda cewa "idan mai kare wanda ake zargi nafarko (yusuf) tanada magana da shaidar da aka gabatar, zata iya mikewa", sady tamike tareda gyara zaman rigarta tadubi dan tashe tace "sd dan tashe kace kasan abba sosai harma kafadi wasu daga cikin halayensa", "eh hakane nasanshi farin sani" dan tashe yafada, "shekarunku nawa tareda abba", "akalla munkai shekara biyar zuwa shida" dan tashe ya amsama barista tambayarta, "kuna tareda abba ne alokacinda akace wannan abu yafaru?", sady takuma tambayar dan tashe, "aa gaskiya bamu tare kuma bansan inda yatafi ba sbd nima na nemeshi a lokacin banganshiba kuma nakira wayarshi bansamu ba", dan tashe yafada "to dakanemi wayarshi baka samuba ko kaje gdansu nemansa?" sady takara tambayar dan tashe, "a'a bantaba shiga gdansuba balle inje daniyar nemansa, duk idan ina nemansa muna haduwa ne a majalisa".... "Ya mai shari'a yakamata kotu tayi duba izuwa zancen wannan mutum wanda yake ikrarin yasan abba farin sani amman baitaba shiga gidansu ba to tayaya zaisan halayensa, inaso kotu tayi watsi da wannan shaida sbd babu makama acikinta" sannan tadan rusuna kanta tareda fadar "nagode ya mai sharia" tana gama magana takoma tazauna... Bayan alkali yayi yan rubuce rubucensa dayasaba sannan yadago kansa, "idan akwai mai wata magana, kotu tana saurare", barista sady ce takara mikewa tsaye "inaso kotu tabani umarni domin zantawa da abba", "anbaki dama" alkali yabata amsa,.. "abba kamar yadda ka tabbatarma kotu dacewa anbaka yasmeen amatsayin wadda zaka aura, shin ku kuka hada kanku kokuwa iyayenku ne suka hadaku?", "Iyayenmu ne sukayi wannan shawarar", "Objection ya mai shari'a, banyadda da maganganun da ake tuhumar abba dasuba sbd basu shafi wannan shari'ar ba" barista auwal yafada tareda mikewa tsaye, yana karasawa kuma yakoma yazauna, bayan yazauna ne sai barista sady tamike "ya mai shari'a inaso kotu tayi watsi da wannan korafi saboda babu wanda yasan dalilin faruwar wannan abin, kuma wannan ba karamin case bane zai iya shafar duk inda ba azato", "korafi bai karbu ba" cewar alkali, "nagode ya mai shari'a" sady tafada tareda juya agun abba "abba lokacinda aka shaida maka za ahadaku kaida yasmeen, kasan abinda ke tsakaninta da yusuf?" sady tatambayi abba, "eh nasan abnda ke tsakaninsu", "meyasa kakeson aurenta dukda kasan tanada wanda takeso?", "saboda bazan iya juya hannun kyautarda alhaji yayimanba, idan naki amincewa kamar na nuna rashin godia ne kuma nima inasonta", abba yafada, "itama ta amince kamar yadda ka aminche da zabin iyayenku, kokuwa ta kawo gardama acikin maganar?", "a'a batayi gardama ba amman har bayan anhadamu bata fidda son yusuf a zuciyarta ba" abba yabata amsa... Ya mai shari'ah ina fatan kotu ta fahimci acikin zancendanayi da abba ya tabbatar mana dacewa yasanda yusuf amatsayin saurayi ko ince masoyin yasmeen ne. Idan kotu tayi duba da abinda ke tsakanin yusuf da abba dakuma yasmeen, shi zai nuna mana cewa abba ne yayi laifin, sbd hakane ma yasa lokacinda suka kashe aliyu suka kyale yusuf batareda sunyimai ko kwarzane ba amman akayi yunkurin kashe idi mai gadi, dan agoga ma yusuf wannan laifin tareda chusa kiyayya tsakanin yusuf da yasmeen, saboda zatarinka yimai kallon wanda yakashe mata dan uwa, shikuma abba yasamu abnda yakeso kenan, sai ya aureta batareda wata fargaba ba sbd shima yana sonta kamar yadda yafada ma kotu abaya" barista takara gyara tsayuwa sannan tace "wannan shine mabudin dumbin hujjoji da shaidun da nike tafe dasu agaban kotu kuma zan gabatar idan kotu tabani umurni"..... [11:57PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: Part31... "barista auwal ko kanada wata magana ko tambayoyinda zaka iya yima wannan shaida", barista auwal yamike tsaye yadubi indo yace "malama indo shekararki nawa kina aiki a gdan alhaji?", "shekarata 8 gidan alhaji", "tsawon shekarunda kikayi kina aiki a gidan, shin kintaba jin wata yar hatsaniya ta tashi a gidan", "gaskiya zaman lafiya akeyi a gidan alhaji rigima bata taba kaurewa a tsakaninsu ba" indo tafada tana girgiza kai, barista auwal yayi wani gajeren murmushi sannan yajuya agun alkali "ya mai shari'a abisa tambayoyin danayimata sun nuna cewa shedar da wannan baiwar Allah tabayar karyane kawai takeyi, kirkirarren labarine sbd ita dakanta tashaida ma kotu cewa gidan alhaji zaman lafiya akeyi sashensu yanason sashe shiyasa babu wanda yataba jin kansu, to tayaya wa'anda sukeyin irin wannan zaman zasuyi yunkurin kashe junansu, yakamata kotu tayi watsi da wannan shaida" yana gama surutunshi yayi godiya yasamu wuri yazauna, alkali yakuma yin rubutunshi na al'ada daga bisani kuma yadago kansa "barista sady kinada wata tambaya dazakiyi?", barista tamike tareda fadar "a'a ya mai shari'ah iyakar tambayoyin dazanyimata kenan", sannan tamaida dubanta akan indo tace "mungode malama indo zaki iya komawa mazauninki kizauna idanma kinada uziri a gida zaki iya tafiya" tana gama magana kuma takara juyowa agun alkali "ya mai shari'a inaso kotu tabani izni domin gabatar da shaidata ta gaba", "kotu tana saurare" alkali yafada, "kotu tana bukatar ganin inspector jabir", cikin bakaken kayan police ya ratso kotun tareda wasu mutane guda ukku wa anda suke a daure, bansan ko suwaye ba amman nayi mamakin yadda naga abba ya gigice dalilin bayyanar wa'annan mutane, bansan abinda yabashi tsoro ba, police din koko mutanenda ke adaure, bankarasa tunaninda nakeyiba natsinto muryar barista sady tana magana "inspector dukda dai gaka acikin kayanka amman kotu tana bukatar saninka da aikinka", "sunana inspector jabir aliyu dodo ina aiki ne a state c.i.d dake modoji a garin katsina" inspector yagyara zaman hularsa lokacinda yake karasa maganarsa, "inspector jabir wa'annan mutanen fa?" sady tafada tareda nuna mutane guda ukku wa anda suke adaure "mun kamasu ne a ranar asabar 09-8-2014 muna cikin aiki a dadai round about din dake g.r.a, muka tsaida wata mota domin yin aikinmu kamar yadda muka saba, bayan mungama bincikar motar sai wadda take acikin motar tashaida mana, itafa tunda ta taho talura dawata mota tana binta a baya kuma batasan ko suwanene ba, ta fadamana number motar muka shiga muna dubawa daga cikin motocin dasukayi layi suna jiran mu tantance su domin susamu wucewa, cikin ikon Allah muka samu motar da wannan mata tafada mana, bamuyi kasa a guiwa ba muka damkesu muka nufi station dasu domin sanin dalilinda yasa suke binta, munsamu makami acikin motarsu wa anda suka hada da bindiga pistol 9.9m dakuma wuka, saida muka tsananta bincike sannan suka fadamana anturosu ne domin su kasheta kokuma su nakasata yadda bazata kara yima kanta amfani ba balle tayima wani, saboda basu so taziyarci shari'ar da ake gudanarwa azama nagaba a matsayinta na lauya", "mungode inspector jabir da wannan kokari naku, tunda ka kawomana su zaka iya komawa kazauna idan muna bukatar wani bayani zamu kira ka" sady tafada sannan tajuya agun mutanen guda ukku wa anda suke daure da ankwa, tadubi nafarko tace "bawan Allah minene sunanka", "sunana takwalale", nabiyun kuma yace "sunana turwa", sannan tamatsa agun na ukkun kaifa ya sunanka "sunana mun lume", barista sady takara dacewa "minene hadinku da wannan shari'a har kukayi kudirin tsaida ita tahanyar kashe daya daga cikin wakilan wa anda ake zargi?", "bamune muka sanya kanmu ba sanyamu akayi ta hanyar biyanmu kudade masu yawa" barista sady takara gyara tsayuwarta tareda fadar "wanene yasanya ku wannan aikin?", "hajiya bilki" yafada cikin wata kakkausar murya. Sannan barista tajuyo agun alkali tace "ya mai shari'a inaso kotu tabani dama ta karshe", "kotu tabada dama", "kotu tana son ganin malan idi" barista tafada tana kallon idi mai gadi, ba tareda bata lokaci ba idi ya hallara, "malan idi ko kasan wa'annan" barista tafada tana kallon idi, idi yadubesu daya bayan daya sannan yace "tayaya zan manta da wa'annan fuskokin, sune wa'anda sukayi yunkurin kasheni", "tambayar dazanyimai kenan ya mai shari'a" barista tafada sannan tajuya agun alkali tayi godiya, "barista auwal kanada wata magana?" alkali yafada yana kallon inda lauyoyin guda biyu suke azaune, "a'a ya mai shari'a duk hujjojin data kawo sunyi daidai da shaidun ta suka gabata" barista auwal yafada kanshi yana kallon kasa, "abisa hujjoji dakuma shaidu dasuka gabata agaban kotu, kotu ta gano cewa yusuf bayada laifi sbd haka kotu ta wankeshi, kuma kotu ta yankema abba hukuncin kisa ta hanyar rataya kasancewar shine wanda yakashe aliyu da hannunshi, wa'annan mutane guda ukku tareda hajia bilki za'a zaunar dasu a gidan kaso har tsawon shekaru 25. Idan kuma akwai wanda yakeda bukatar daga kara zuwa kotun gaba, yanada dama kafin kwana30. Kooootu!!!... [11:57PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: ALKAWARI Part30..... Tana zuwa nan dazancenta sai tayima alkali godiya tasamu wuri tazauna, "barista auwal kanada wata shaida wadda zaka sake gabatarwa?" alkali yafada yana kallon inda lauyoyin suke azaune, "eh ya mai girma mai shari'ah" barista auwal yafada lokacinda yake mike tsayewa, sannan yayi gyaran murya tareda fadar "inaso ingabatar da shaidata kwakwkwara wadda take nuna wanda yayi wannan aikin baro baro, wadda itace wukar da akayi amfani da ita wurin kashe aliyu, kuma anyi bincike angano zanen hannun yusuf ne kadai yayi amfani da wannan wuka" yana gama fada sai yamikoma maga takarda wukar, maga takarda kuma yamika ma alkali, bayan alkali yagama dubawa sai yabuda baki yace "barista sady ko kinada ja dangane da wannan shaida da dayan bangaren suka gabatar?", "a'a ya mai shari'ah" sady tamayarwa alkali da amsa, sannan alkali yadubi barista auwal yace "kotu tana sauraren hujjarka ko shadarka ta gaba", "iyakacin shaidata ta kenan ya mai girma mai shari'ah" barista auwal yafada tareda yin godiya gami dazaunawa a mazauninsa. Alokacin alkali yakuma gyada kanshi a rukuninda lauyoyin suke azaune "barista sady kotu tashirya sauraren hujjoji dakuma shaidunki", yana gama magana barista sady tamike "kotu tana bukatar ganin karime" batare da bata lokaciba karime ta bayyana agaban kotu, "karime kotu tana bukatar sunin ko ke wacece" sady tafada "suna na karimatu salisu kuma ni yar asalin garin agadaz ce" karime tafada tana kallon sady, "ke yar agadaz ce to me yakawoki agarin katsina" sady tafada da alamar tambaya karara a fuskarta, "nabaro garinmu nashigo nigeria ne kasancewar rashin karfi damuke dashi gdanmu shiyasa nabaro gida dan nema mana abnda zamu rike kanmu da yan gidanmu", "kinaso kice neman kudi ne yakaiki har gidan alhaji jafar kenan" sady tafada, "eh hakane sbd ina daga cikin yan aikin gidan wa anda ake biya duk karshen wata" karime tabada amsa tana gyada kai, "malama karime ance tunda kika tafi ganin gida baki kara dawowa ba, kinsamu kudinda zasu isheku keda sauran yan gidanku ne koko?", "a'a gaskiya nabar gidan Alhaji ne batareda niyar dawowa ba sbd wata matsala dana lura tana niyar samun gidan, kuma nasan idan matsalar tafaru harmu yan aiki bazamu tsira ba" sadda tazo nan da zancenta sai tayi ajiyar zuciya sannan kuma taci gaba da magana "ranar wata laraba ina zaune sai mai dafa abnchi(kuku) ya umurceni da inkaima abba abnchi a dakinsa kamar yadda yabukata, bayan na hada komai nanufi dakinsa ina zuwa daidai kofa sai najiyo muryar aunty bilki tana magana daga cikin dakin "kana tunanin zamu barsu ne suma suci gaba da rayuwa? kai basu kadai bama, dukwanda yatsaremana hanya shima sai ya bakunci lahira......" karime na gama zancenta sai barista sady tadubi alkali tace "iyakar tambayar dazanyimata kenan ya mai shari'ah", "barista auwal ko kanada tambayar dazakayima shaidar da aka gabatar?" alkali yafada, "eh ya mai shari'ah", "karime shekararki nawa kina aiki a gidan alhaji jafar?" barista auwal yatambayi karime, "cikin shekara ta ukku ce wannan", "lokacinda kikaji abnda su abba suke fada a daki meyasa baki fadama alhaji abnda ke faruwa ba, kokuma kisanarda hukuma hakan?", "gaskiya bazan iya tunkarar alhaji infadamashi wannan maganarba sbd banida wata hujja mai kwari, idan nayi haka nice zanshiga cikin matsala, shiyasa ma nayanke shawarar barin gidan domin gudun abnda zaije yadawo, amman lokacinda zantafi na fadama abokiyar aikina indo duk abnda ke faruwa tareda alkawarin bazata fadama kowa ba", "zaki iya fadamana inda abokiyar aikin taki take?" barista yafada yana kallon karime, "eh nama ganta acikin kotunnan" karime na bayarda wannan amsar sai barista auwal yacema alkali "iyakar tambayoyin dazanyimata kenan ya mai shari'ah".... Barista sady tamike tace "nagode karime zaki iya komawa kizauna", sannan tajuya agun alkali "ya mai shari'ah ina neman iznin gabatar da shaidata ta gaba", "anbaki izni", alkali yafada, "kotu tana bukatar ganin indo", batareda bata lokaciba indo tahallara agaban kotu, "malama indo kotu tanaso tasan ko ke wacece dakuma aikinki" barista tafadama indo, "sunana a'isha amman anfi sanina da indo, ina daga cikin masuyin hidima agidan alhaji kamar yadda karime ta gabatar, nima ina daya daga cikinsu", "malama indo kinji abnda karime tafada shin dagaske ne abnda tafada koko?" barista ta tambayi indo, "eh tabbas yadda tafadamun haka ta fadama kotu kuma ta gargadeni dakar infadama kowa, kuma nima na gasgata maganarta saboda akwai wata rana da daddare aka umurceni da inkaima usman abnci yana falo, akan hanyar kai abncin ne nahadu da aunty bilki tana tafiya tana surutu amman nadanji kadan daga cikin abnda take fada, "(eh mu muka kasheshi din kuma saima munga bayan dukwanda ke gidannan)", tabbas naji wannan kalami daga bakinta har saida nazubar da kwanonin abncin dake ahannuna sbd tsabar storota danayi, amman nafake da tuntube nayi" indo takarasa maganarta lokacinda take gyara zaman wuyan hijab dinta.... [11:57PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: ALKAWARI Part32... "hujjoji dakuma shaidu dasuka gabata agaban kotu, sun tabbatarda cewa yusuf bayada laifi sbd haka kotu ta wankeshi daga wannan zargi, kuma kotu ta yankema abba hukuncin kisa ta hanyar rataya kasancewar shine wanda yakashe aliyu da hannunshi, wa'annan mutane guda ukku tareda hajia bilki za'a zaunar dasu a gidan kaso har tsawon shekaru 25 tareda tarar kudi naira dubu dari, akan kazafin da akayima yusuf. Idan kuma akwai wanda yakeda bukatar daga kara zuwa kotun gaba, yanada dama kafin kwana30. Kooootu!!!... Haka kowa yawatse tareda mamakin yadda wannan shari'ah takasance mai kama da wasan kwaikwayo, muma muka dunguma muka nufi gida cikin murna, bawani dadewa nayiba a kurkuku sbd ban kwashe wata ukku ba amman naga garin ya canza man hatta iskar danike shaka tasha banban da iskar gidan maza... Ba karamin farin ciki mukayiba awannan rana wanda idan natsaya fadamaku sai munbata lokaci dayawa.... Bayan wani dan lokaci da faruwar wannan lamari tun ba ayi nisa ba soyayyata da yasmeen tadauko wani sabon salo wanda aduk rana idan daya baisanya daya acikin idonshi ba to ranar babu kwanciyar hankali, hatta wayoyinmu sunshaida hakan sbd muna wahalar dasu, wurin kiraye kiraye... Kwance nake a daki da misalin karfe 11 na dare, har bacci yafara dauka ta naji wayata tana ta faman ruri, ko dubawa banyiba kawai nadauka tareda kangawa a kunne na, salamu Alaikum nafada, "wa alaikassalam" aka fada daga dayan bngaren tareda wata yar gajeriyar daria, hakan yasa nagane ko dawa nike magana sbd nasan muryar kamar yadda nasan kofar baki na, mutum yana baccinshi mai dadi anwani tadashi, "hmm hakama zakace ko to shikenan sai dasafe" aka fada daga dayan bngaren. laaaaa dan Allah yi hakuri bafa dake nike ba, ai kema kinsan duk dadin bacci baikai dadin muryarki ba, nafada tareda mikewa zaune, "to idan badani kakeba dawa kake?" nifa da saurayen(mosquetoe) gidanmu nike magana, sune sukazo saman kaina sunata yiman waka har suka tadani, "bawani nan! Saurayen ne zasuyimaka waka?", eh mana ko in reramaki kiji, "eh yiman inji idan gaskiya ne", buuuuuuuu! Tunkafin inrufe bakina naji sautin dariyarta yadaki dadon kunne na, nima sai natayata muka idarda dariyar tare. "oh kai Allah yashiryeka" tafada tana murmushi, sannan takara dacewa, "daman dady ne yace inyimaka magana kazo gobe yanason ganinka", na nunamata jin dadina sosai daganan kuma mukaci gaba da firarmu irinta masoya..... Wan shekare da misalin karfe 9am natashi nasanya ruwan zafi kasancewar safiyar ranar ana wani irin sanyi mai tattare da iska sakamakon ruwan saman da aka malala cikin dare, bayan nayi wanka nashirya tsaf wurin 10am natafi domin amsa kiran mahaifin yasmeen..... Ina shiga natarar dashi zaune akan kujera ya daura kafa daya akan daya yana kallon jarida tacikin siririn farin gilashin dake sanye a fuskarsa. Bayan nagaidashi gaisuwa kamar yadda yadace na saurara inajiran dalilin kirana. Wani dogon numfashi yayi tareda linke jaridar dake hannunsa "yusuf nasa ankiraka ne sbd wata magana danikeso inyi dakai" yakarasa maganarshi yana kallona, sannan yaci gaba da magana "na fahimci abnda ke tsakaninka kaida diyar wajena, nayi bincike akanka yadda yakamata, daga ciki har nagano ku ba yan asalin garinnan bane daga maiduguri kukazo, kuma mahaifinka ya dade da rasuwa, hakane?" yakarasa maganarshi da alamar tambaya, eh hakane alhaji, nafada batareda nadago kai na kalleshi ba, "yusuf aikin me kakeyi yanzu?" lokaci guda jikina yadau kyarma sbd bnyi tsammanin wannan tambayar ba saboda nidai nasan banida wani aiki amman dakyar natsinci kaina ina fadar, banida wani aiki alhaji, "to wane mataki kake acikin karatunka?", na gama secondry amman karatun yatsaya sakamakon rashin karfi kuma... "what!" muryarshi naji tayi tsalle ta daki dodon kunne na, hakan yasa nayi shiru batareda nakarasa maganar danakeyi ba. "kana nufin ahaka kake neman diyar tawa batareda kanada wata madafa ba" yana magana ne cikin mamaki, "to bari kaji infada maka ni bahaka nikeba, saboda bazan iya sayar da akuya ba kuma tadawo tana ciman danga" yafada lokacinda yake zare gilashin dake sargafe a fuskarsa "daga yau na rabaka da diyata babu kai babu ita, kaje kasamu daidai dakai amman ba a gidana ba" yafada tareda mikewa tsaye yanufi hanyar fita waje, har yakai bakin kofa sai yatsaya, "kuma idan baka rabu da itaba zandauki mataki mai tsanani akanka" yafada batareda yajuyo yakalleni ba, nikau tuni na dade da mutuwa daga zaune narasa minene kemun dadi, wani sabon gumi yarinka fita daga jikina zufa tayiman kawanya, tareda wasu zafafan hawayene dasuka rinka ambaliya akan fuskata, hatta lumfashinda nakeyi zafinshi ya tsananta acikin kofofin hancina... Dakyar nasamu nafiddo kaina daga cikin dakin, ina fitowa nahadu da yasmeen, hankalinta yatashi ganin yadda nafito a kidime shiyasa tayi gaugawar jifata da tambaya "me yafaru naganka haka?" shiru nayi ina kallonta nakai dakika biyar ina neman sulhu acikin zuciyata, akan infada mata gaskiya wani bangaren nadaga zuciyata kuma yana cewa a'a...... [11:57PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: 33/34ALKAWARI Part33...... Ina fitowa nahadu da yasmeen, hankalinta yatashi ganin yadda nafito a kidime shiyasa tayi gaugawar jifata da tambaya "me yafaru naganka haka", shiru nayi ina kallonta nakai dakika biyar ina neman sulhu acikin zuciyata, akan infada mata gaskiya wani bangaren nadaga zuciyata kuma yana cewa a'a, bansan lokacinda zuciyata tagama wannan tattaunawar ba saidai kawai naji har anyanke hukunci natsinci bakina yana fadar. kaina ne yakemun ciwo, dukda dai nasan badole bane ta yadda da abinda nafada ba. "haba yusuf me kadaukeni ne, kaima kasan babu abnda bansani ba dangane dakai" sannan tayi ajiyar zuciya daga bisani kuma taci gaba da magana "ko acikin duhu bazaka iya boyemun damuwarka ba, me yasa kakeson boyemun abnda ke damunka ne", dady ne yace dole sai na rabu dake, maganar tafito daga bakina tareda wani kululu wanda baisamu damar fitowa ba saidai yatsaya acikin makoshi na, "ka kau san abinda kake fada?", na sani nima ganin abin nakeyi kamar a mafarki, daidai lokacin hawaye suka samu damar gangarowa akan fuskata, itakau tsaye take tabude baki kamar zatayi magana amman ta kasa, sai hawayen da keta zirga zirga daga idanuwanta zuwa fuskarta, juyawa nayi da zummar ficewa sai naji ta riko hannu na, "haba yusuf kayi tinanin da gaske ne?, wlh dawasa dady yake yimaka, yaza ai arabani dakai bayan bazan iya wata rayuwa idan batare dakai ba, dan Allah kada katafi" cikin kuka take zayyano kalamanta cikin wata irin murya kalar tausayi, dole tasa najuyo nakalleta fuskokinmu duk sunyi share share da hawaye, kiyi hakuri yasmeen babu maganar wasa aciki, wannan kaddara ce Allah ya dora mana babu yadda zamuyi kuma yazama dole mubi maganar iyayenmu, "haba yusuf ya kake zaton rayuwata zata kasance idan babu kai? Zuciyata fa kamar shukar ayaba(banana) ce, sau daya takeyin 'ya'ya, idan tayi sau daya to tagama amfani saidai a sareta kokuma abarta domin kwalliya. Nima haka nike zuciyata zabi daya takeyi kuma soyayyata guda daya ce" , to yanzu yakike so muyi? Na tambayeta tareda kuramata ido, "sai mugudu mubarmasu garin mutafi can wani wuri inda babu wanda yasanmu muyi rayuwarmu acan" takarasa maganarta tareda kara matse hannu na dan karma inkubce mata. Haba baikamata kifurta wannan maganarba ko dawasa kada kikara tunanin fita daga gidan mahaifanki batare da izninsu ba, "aan ya kake kokarin juyamin baya dan Allah kayarda mutafi, idan duniya tajuyamun baya kaine kadai zaka karkato agareni insamu sassauci, amman idan kajuyamun baya ko duniya damutanen cikinta suka karkato zuwa gareni bazasu amfaneni dakomai ba. Dan Allah kada kabarni". Haba yasmeen duk irin so da kaunar danikeyi maki batakai irin sonda iyayenki sukeyi makiba, kada fa kimanta ta hanyarsu kikashigo duniya, sukayi renonki tun bakisan ko ke wacece ba harkika san kanki, ci da sha sutura, babu irin kulawar da basuyi maki, yasmeen ta yaya zaki hada soyayyar wa'annan da soyayyar wani, ko kin manta azabar da Allah ya tanadar ma wanda ya bijirema iyayensa, "ya kake magana da wadda tinaninta yakoma bin zuciyarta Ya kake kokarin fahimtar da wadda kwakwalwarta ta toshe da soyayyar zabin zuciyarta, yanzu bazan iya hakuri ayi kokarin rabani dakai ba" takarasa maganarta tana girgiza kai, ko kadan bazan iya rabuwa da iyayena ba kuma bazan sanya kirabu da naki iyayenba, saboda nasan dole muyi nadama a lokacinda baza8 taimana amfani ba, har na juya natafi sai naji tana rera wani irin kuka cikin wani kalar sauti mai matukar karya zuciyar dukwanda yayi tozali dashi acikin dodon kunnenshi, bansan lokacinda najuyo nadawo a gareta ba, "kiyi hakuri yasmeen Allah8 yana tare damu kidauka wannan jarabawa ce agaremu. Adai dai lokacin nafiddo zoben dake sanye a danyatsana, nasanya mata ga hannunta najuya natafi, inaji tana kiran suna na amman bazan iya amsa kirantaba a wannan lokacin......Tu nda nashiga gida banyima kowa magana ba nawuce dakina nakwanta cikin wani irin yanayi wanda bazan iya misaltamaku ba amman dukwanda yaganni yasan ba cikin hayyacina nike ba, duk yinin ranar haka na kasance banida aiki sai tinane tinane wani lokacin kuma zuciyata tarinka yiman tambayoyinda bansan amsarsu ba, "wai meyasa rayuwata take cike da wahala da kunci? me nayima Allah ne yake jarabani da hali mafi wuyar jurewa? Wani bangaren nadaga zuciyata kuma yana shaidamun cewa "kadaina irin wannan tinanin domin gujema fushin uban giji. Basai na fadamaku halinda yasmeen tashiga ba sbd zamu8 bata lokaci sosai, amman damuwarta tafi tawa.... Sati daya da aukuwar wannan kaddara a garemu tunda safe na nufi dakin umma da niyar ingaidata kamar yadda nasaba a kowace rana... "haba yusuf meyasa kakeda rikon abu a zuciyarka ne, ko so kake kadorama kanka hawan jini tun kana dan kankane duba kaga yadda ka rame, duk kabi ka kanjame kamar wani mai ciwo" umma ce take magana cikin sigar fada, muna cikin wannan yanayin ne sai mukaji anyi sallama, Salamu alaikum!!!......... [11:57PM, 23/09/2016] ✨@lh@ji✨: ALKAWARI Part34.... "haba yusuf meyasa kakeda rikon abu a zuciyarka ne, ko so kake kadorama kanka hawan jini tun kana dan kankane duba kaga yadda ka rame, duk kabi ka kanjame kamar wani mai ciwo" umma ce take magana cikin sigar fada, muna cikin wannan yanayin ne sai mukaji anyi sallama, Salamu alaikum!!!... Gaba daya muka amsa tare da juyawa domin ganin wanda yake shigowa, "sannu dazuwa halimatu" umma ce take magana acikin fara'a. Banyi mamakin ganin haleematu ba sbd tunda muka fito kotu tana dan zuwa jefi jefi tana gaida umma. Bayan sungama gaisawa ne tabukaci komawa gida, sukayi bankwana takama hanyar fita nikuma nabita abaya nadan ta ka mata har zuwa inda tayi packing din motar ta "yusuf wurinka nazo sbd wata guguwa datake neman tasowa ta tarwatsa duk abnda nake kokarin tanadarwa", halimatu ce take magana cikin damuwa. kamar yah kenan halimatu bangane inda kika nufa ba, nafada tareda zakuwa domin jin bayanin daza tayiman in fahimta, "wai aure za ayiman" tafada tareda jinjina maganar, iyyeh! kice munkusa shan shagali kenan, nan gaba kadan zandaina kiranki da halimatu saidai ince amarya, "haba yusuf kana tinanin zan auri wanda bana so ne?". Kina nufin bakison wanda mahaifanki suka zaba maki kenan, "gaskiya ni bana sonsa" takarasa maganarta tareda girgiza kai. Halimatu kada soyayyar wani tarufe maki ido har tasa kiwuce zabin da iyayenki sukayi maki kuma ki ketare umurnin da addini ya tsara mana, "kaima ka goyi bayan a auraman wanda bana so kenan" tafada kamar mai shirin yin kuka, ba haka bane kinsan yazama dole mutun yabi iyayensa indai har yana son yasamu tsira. Ko kinmanta da hadisin da Umaimata (R.T.A) ya ruwaito wanda yake cewa: Hakika wani mutum ya tambayi manzon Allah: "Ya Manzon Allah, menene HAKKIN IYAYE AKAN DANSU??? Sai Manzon Allah (S.A.W) yace Sune "ALJANNARKA DA WUTAR KA.... Kuma awani hadisin manzon Allah yana cewa: "kubauta ma Allah shikadai kada kuhadashi dawani abu awurin bauta, kuma ku kyautata ma iyayenku". "tabbas hakane kuma nasani aljannar 'ya'ya tana karkashin iyayen su" sannan tayi ajiyar zuciya daga bisani kuma taci gaba da magana "amman kasani zanbi iyayena ne idan har basu sabama addini ba, idan kuma suka kauce to bazantaba binsuba. bazanyadda in auri wanda baniso ba, dan kowa yasan acikin addini babu auren dole sbd A lokacin Manzon Allah anyi wani mutun da ake kira da suna Mughir wanda Allah ya jarrabe shi da tsananin son wata mata da ake kira da suna Barira, amma kuma cikin ikon Allah ita kuma duk duniya babu wanda bataso irinsa (Mugheer), har saida takai yana bin ta a hanya, yana kuka, yana rokonta da ta soshi, amma ita kuma ta kekasa kasa. Watarana sahabbai suka ga irin halin da mughir ke ciki, suka cewa manzon Allah shin baza kashiga cikin al’amarin Mughir da Barira ba, Manzon Allah Salallahu Alaihi Wasallam, da kansa yace hakika anjarrabi Mughir da soyayyar Barira. Manzon Allah ya taka da kafarsa mai daraja, yaje wajen barira da kansa, ya ce yanzu barira baza kiso Mughir ba! Ta ce ya Manzon Allah! kana bani umarni ne, ko kuma kana bani shawara, yace ina baki shawara ne, ta ce ya Manzon Allah bana sonsa, haka Manzon Allah ya taso yana mamakin irin yadda zuciyar Barira bata nutsu da Mughir ba duk kuwa da irin yadda yake nuna soyayya a gareta. Kaga kenan da auren dole yana da muhalli a musulunci da Manzon Allah ya umarci Barira ta auri Mughir sai dai baiyi hakan ba. Wannan shi ya nuna mana cewa addinin Musulunci bai yarda da auren dole ba, domin da ana yi, da saboda yadda Manzon Allah ya tausayawa Mughir da ya umarce ta da ta aureshi". Tana zuwa nan da zacenta sai tayi shiru. To yanzu me kika fadama mahaifanki?, "kwana biyar 5 suka bani domin infitar da wanda nike so, idan lokaci yayi ban fitar ba, zasu auramin wanda ransu yake so", sai ki gaggauta fitar da zabinki kafin suzabar maki, "saidai wanda nike so haryanzu baisan abnda nikeyi ba, na budamai zuciyata amman ya kasa fahimta ta, na nuna mai amman yaki ganewa" alokacin wasu yan hawaye suka samu damar gangarowa akan fuskarta, nakalleta cikin tausayi tareda fadar, ya kamata ki gaggauta fadamai kafin lokaci yakure maki. Rufe bakina yayi dai dai da saukowar ruwan sama, cikin sauri nayimata bankwana tashige mota ta tafi nikuma na karkata kafafuwa na zuwa gida... Zaune take akan gado tana kallon kyakykyawan zoben azurfar dake sargafe a dan yatsanta, tahada kai da guiwa tanata rera abinta kamar yadda tasaba, da ace bangon dakinta zaiyi magana to da zai iya rera irin kukan bakin cikin data dade tana rerewa ba dare ba rana, turo kofar da akayine yasanyata dago fuskarta dasauri. "wai me kike so kizama ne yasmeen, ko kinaso kinuna mana kinfimu sanin abnda yadace" yana maganarsa ne acikin fada, "a'a dady bahaka nike nufi ba" tafada cikin wata dakusasshiyar murya tana sarkewa, "nasan yadda kikeji amman kisani nayi hakane domin......... [12:02AM, 24/09/2016] ✨@lh@ji✨: Part35....... Zaune take akan gado tana kallon kyakykyawan zoben azurfar dake sargafe a dan yatsanta, tahada kai da guiwa tanata rera abinta kamar yadda tasaba, da ace bangon dakinta zaiyi magana to da zai iya rera irin kukan bakin cikin data dade tana rerewa ba dare ba rana, turo kofar da akayine yasanyata dago fuskarta dasauri. "wai me kike so kizama ne yasmeen, ko kinaso kinuna mana kinfimu sanin abnda yadace" yana maganarsa ne acikin fada, "a'a dady bahaka nike nufi ba" tafada cikin wata dakusasshiyar murya tana sarkewa, "nasan yadda kikeji amman kisani nayi hakane domin nema maki mazauni wanda yadace dake, ko kadan bazanyadda inkaiki inda zakisha wahala ba, sanin kanki ne wannan yaron bayada sana'a kuma karatunma bayi yake ba tayaya zai rike kanshi balle har yakula dake, ko kintaba ganin inda akaci soyayya a zaman aure?" shiru kawai tayi tana sharbar kukanta, bai tsaya jin amsartaba yamike daniyar tafiya, "wlh ina sonshi dady inasonshi ko ya yake kuma zan iya zama dashi a haka, dan Allah kutaimaki rayuwa ta" siririyar muryar matashiyar taci gaba da fitowa tareda kuka, ko saurarenta baiyiba yaja kafafuwansa yanufi hanyar ficewa daga dakin, "ina sonshi! Wlh ina sonshi" dakarfi tayi magana yadda har nawaje zai iya jin abnda take cewa, yana fita daga dakin yajingina da kyauren dakin diyar tashi cikin nadama dakuma tausayin halinda yasanya diyarshi dakanshi, wani sashen na zuciyarshi yana bashi shawarar yazama dole yanemamata farin cikinta idan ba haka ba zai iya rasata, baisan lokacinda yatura kofar dakinba tareda kutsa kai cikin dakin yaci gaba da magana ahankali cikin sanyin rai "kiyi hakuri yasmeen bawai ina nufin rabaki da wanda kike so bane, nayi hakane domin daukar mataki akanshi indai yana sonki da gaskiya to hakan danayimai shi zaisanyashi jajircewa tareda neman abin kansa, amman ko kusa banyi hakaba domin rabaku kokuma sanyaku acikin wani hali ba" ya karasa maganarsa yana jira yaga hankalin diyar tashi ya kwanta amman ga mamakinsa sai yaga kwance take ko alamar lumfashi babu atare da ita, cikin sauri yakarasa agunta tareda yimata wani irin kira guda ukku a jere, yasmeen! yasmeen!! yasmeen!!! Cikin hanzari ya kwasheta zuwa asibiti.... Tsawon lokacinda likitoci suka kwashe sunata fafutukar ceto rayuwarta yasanya alhaji da sauran iyalansa kaguwa domin jin halinda yarsu take ciki, zaune suke akan kujerunda aka tanada cikin asibiti musamman domin irin haka... Wani dan siririn likita yafito tareda nufowa inda suke, tunkafin yakaraso alhaji jafar ya tarbeshi "doctor ya jikin nata? Ta tashi?", "munyi iya kokarinmu domin ganin munceto rayuwarta sbd zuciyarta ce tabuga sakamakon wani mawuyacin hali data shiga, la'alla wurin wani dogon tinani kokuma sanadiyar rasa wani abu datayi, wanda hakanne yayi tasiri wurin samun matsala a wani sashe na zuciyarta" likitan yafada a tsanake cikin kwanciyar hankali, "to doctor yanzu ya ake ciki kenan" alhaji yayi magana tareda cire hular dake saman kansa, "munyi iya kokarinmu yanzu haka ma tananan kwance Kuma idonta biyu, tanajin magana tana ganin abnda yake wakana, saidai bazata iya komai dakanta ba, ko magana bazata iya yiba, kuma idan tayi 3hours acikin wannan yanayin batareda ta farfado ba, to gaskiya saidai ayi hakuri da ita", "innalillahi wa inna ilaihirraji'un doctor yanzu minene abin yi?" usman yafada tareda mika hannuwa guda biyu biyu agaban doctor kamar wanda zai amshi wani abu, "gaskiya yazama dole asamu abnda zai maye gurbin abnda yasanyata cikin wannan halin, idan wani abu tarasa, yakamata ayi gaugawa a musanyamata dawani abin kamarshi, idan kuma tinanin wani abune takeyi to dole sai annemi hanyarda zata fidda wannan tinanin a ranta koda dai dai na second daya ne, idan kuma wani abune yasanyata cikin bakin ciki to sai ansamu hanyarda za asanyata farin ciki. Wannan ce kawai mafita kuma itakadaice hanyar data rage domin ceto rayuwarta." yana gama fada yakama hanya yawuce, sukuma sukayima dakinda aka kwantar da ita tsinke.... [12:02AM, 24/09/2016] ✨@lh@ji✨: ALKAWARI Part36...... idan tinanin wani abune takeyi to dole sai annemi hanyarda zata fidda wannan tinanin a ranta koda dai dai na second daya ne, idan kuma wani abune yasanyata cikin bakin ciki to sai ansamu hanyarda za asanyata farin ciki. Wannan ce kawai mafita kuma itakadaice hanyar data rage domin ceto rayuwarta." yana gama fada yakama hanya yawuce, sukuma sukayima dakin da aka kwantar da ita tsinke... Sunkwashe tsawon awa guda kowa yana nuna gwanintarsa da fasahar da Allah yayimasu wurin ganin sun ceto rayuwarta amman basuyi nasara ba, saima dai lokaci dayake cin nasara akansu yanata tafiya abnsa. "Alhaji yakamata akirawo yaronnan kilan Allah yasa a dace" mahaifiyar yasmeen tafada tana kallon mai gidan nata kamar zatayimai kuka, baiyi gardamaba wurin amince warsa akirawo yusuf sbd kowa yasan shine ummul aba'isin faruwar wannan al'amari..... Arikice nashigo asibitin ina wata irin tafiya sauri sauri gudu gudu baccinma bansan dakin da aka kwantar da itaba, yazama dole inbi usman abaya saboda shine yasan wurin, da zan iya fallawa da gudu sbd na kagu inje inda take. Ko sallama bamuyiba muka banka kyauren dakin. Suntaru sun zagayeta masu kuka sunayi masu hawaye sunayi, abinda ya bakantaman rai shine, wai harda kayan wasan yara aka kawomata burjat acikin dakin kamar wata jinjira. Alhaji da mamar yasmeen ne tsaye sun daddafe gadon datake kwance, na bubesu daniyar ingaidasu tun kafin inbude bakina naji muryar mahaifiyar yasmeen nashiga cikin kunne na, "dan Allah dannan kataimaka mana kayi iya kokarinka domin ceto rayuwarta, awa ukku likitoci suka bata tun karfe 12 har 2:30 tayi amman shiru bata tashiba", tana magana kamar tana bada umarni tawani bangaren kuma kamar kamar tana neman taimako awurina ganin yadda take miko hannuwa biyu biyu tana langabe kai, lokaci guda tausayinta yakamani ba ita kadaiba, dukma wanda yake acikin dakin sbd hankalin kowa yagama birkicewa. Cikin kyarma nike magana bakina yana rawa, Umma ki kwantar da hankalinki bazata mutu ba, babu yadda za ayi yasmeen tamutu lokacinta baiyiba. "kai kada kamaidamu kana nan yara mana" murya alhaji taci gaba dafita cikin bacin rai, "kaduba kagani likita ya tabbatar mana da wannan abin yakai kasa to shikenan ta mutu" yakarasa maganarsa yana nuni da wata na ura akan wani teburi kusa da gadon, haba alhaji kada damuwarku tasa kumanta da wanda ya halicceku mana, kada wannan yasa ku sabama uban gijinku, kadafa kumanta babu wanda ya isa yadauki ranta sai Allah sbd shine ya halitta abinsa, kuma shine kadai wanda yakeda ikon yin komai, shine yake bayarda arziki ga wanda yaso, shine yake rayawa kuma shine mai kashewa babu abnda likita zai iya yi anan, nafada ta sigar kwantar masu da hankali, amman ina alhaji yayi nisa lokaci guda kuma naji hajiya ta rusa kuka, wasu hawaye suka zuboman, kaiya kaiya dan Allah kitashi domin susan abnda nike fada gaskiya ne. Nafada tareda durkusawa adai dai inda fuskar yasmeen take dan Allah kiyimasu magana domin sudaina yimaki kuka, kingani fa cewa sukeyi mutuwa zakiyi, kitashi domin ki tabbatar masu da ba mutuwa zakiyiba. Nakarasa maganata cikin kuka, lokaci guda dakin yayi tsit kamar babu halittar data taba shigowa. Yasmeen! Yasmeen!! Ki amsa mana ninefa yusuf dinki, ko nima bazakiyiman magana ba? Ko dagaske ne mutuwa zakiyi?. Dai dai lokacin natsinci kaina ina wani irin kuka ciki ciki. Dan Allah kada kitafi kibarni, kada kisa inzama maraya acikin masoya ko kinmanta kece gata na? Kinmanta kece abumai mahimmanci acikin rayuwata? Kinfi kowa sanin bazan iya yin komaiba idan babu ke, murmushina karewa zayayi sbd babu wanda zanyimawa, na tabbata bazan taba samun kaina cikin farin ciki ba sbd kece farin cikina, wace irin rayuwa kikeso inshiga ne? Dan Allah kiyi magana, ki amsaman tambayata mana... Ni ba shirunne yake tadaman hankali ba sbd nasan zan iya zama dake ahaka har tsawon rayuwata, burina kawai kifadamun damuwarki masoyiyata, minene yasanyaki cikin damuwa, gani agabanki na mallaka maki kaine yasmeen wlh bazantaba barinki cikin kadaici ba, kifadaman ko me kikeso ni zanyimaki shi koda kuwa hakan zaiyi silar rasa rayuwata, dan Allah kitashi kada kisa mafarkinmu yazama karya mana, ko kinmanta da yadda muka tsara rayuwar aurenmu? kinmanta burin zuciyarmu na musamu yara kyawawa masu kama dake, haba yasmeen kinmanta da alkawarin dakikayiman cewa zaki tarbiyyantar da yaranda zamu haifa, dan Allah kitashi muci gaba da rayuwarmu. Adai dai lokacin nakamo hannunta ina kuka. Mantawa kikayi da ajiyar zoben danabaki akan zaki maidoman abuna a acikin daren farkon amarcinmu, idan kika tafi kika barni wazai maidoman kenan, wanene zai cika maki wannan alkawarin. Ina magana ina murza zoben dake acikin dan yatsanta tareda wani irin kuka mai shiga zuciya. Su alhaji kau dasauran wa anda ke acikin dakin sunyi tsit suna saurarena kamar masu sauraren wa'azi... "Inna lillahi wa inna ilaihir raji'un!!" doctor yafada lokaci guda kuma yadora hanuwa bisa kai.......... hahaha sorry nandai anyi over act [12:02AM, 24/09/2016] ✨@lh@ji✨: ALKAWARI part37 ...Su alhaji kau da sauran wa anda ke acikin dakin sunyi tsit suna saurarena kamar masu sauraren wa'azi... "Inna lillahi wa inna ilaihir raji'un!!" doctor yafada lokaci guda yadora hanuwa bisa kai, "kuyi sauri ku fiddashi", bangama fahimtar abnda yake nufi ba naji ankama hannuwa na daniyar fiddani waje, lokacin na tsinto maganar alhaji "ya ida kasheta ko??". Dago hannun datayi ne yasa kowa yayi cirko cirko "yusuf kada katafi kabarni" tafada kasa kasa tareda miko hannu tana kallona... Ba karamar murna muka shiga ba ganin ta dawo hayyacinta lokacinda kowa yagama fidda rai da ita, basai na fadamaku irin farin ciki dakuma murna damuka shigaba... Ranar laraba da safe misalin karfe 10am na safe suka kammala breakfast amman dukansu babu wanda yabar dining area din, suna zaune sunata hirarsu irin ta iyaye da 'ya'ya, alhaji jafar ne zaune kusa da matarsa hajia binta, suna fuskantar yaran nasu guda biyu usman da yasmeen, kasancewar ranar antashi dawani irin ruwan sama mai karfi shiyasa alhaji baifita aikiba. "dukanku babu wanda yafadamun abnda yakeso a wannan sallar, ko baku bukatar komai ne a wannan lokacin?", usman yayi carab yace "haba dady aini wannan sallar a saudiya naso inyita, kawai dai...", yajuya agun yasmeen "kefa me kike so?", "ni bani bukatar komai dady" yasmeen tafada tareda maida dubanta ga mahaifin nata. Murmushi kawai yayi sannan yace, "kifadama yusuf din na bashi umarni yaci gaba dazuwa nemanki", a razane tadubi mahaifin nata tana tinanin kodai kunnenta ne yajiyo mata ba dai daiba, bata tabbatar ba saida taji yakara dacewa "kuma kicemai yakawo man credentials dinshi zanduba mai aikinda zaici gaba dayi tareda ci gaba da karatunshi", tayi kokarin saita kanta akan murnar datashiga amman takasa, harsaida bakinta yatonama fararen hakoranta asiri, usman da hajiya kau murmushi suka cigaba dayi da alama dama sunsan da maganar, lokaci guda taji kunya ta rufeta, tasanya hannuwanta tarufe fuskarta. Alokacin alhaji ya kyalla ido ya hango zoben dake makale a hannunta cikin hanzari ya cakumo hannunta kamar zai ballashi yakama dan yatsan da zoben yake yana kallo lokaci guda kuma yasaketa tareda shiga dakinsa cikin sauri. Wannan ba karamin tadama yasmeen hankali yayiba dukda dai batasan abnda mahaifin nata yake nufi ba, nandanan sai gashi ya dawo a firgice yakuma fizgo hannunta yakalli zoben kuma yadubi gudan zobe dake hannunsa babu wani banbanci danashi "ke kifadaman ina kika sameshi", yakara tambayarta acikin tsawa, "haba alhaji kayimata ahankali mana sai tafada maka" hajia binta tafada, yasmeen takwashe komai tafadamai... Daganan suka dunguma su duka suka nufi gidan su yusuf... Muna cikin daki nida umma da hadiza kasancewar tsakar gidan namu duk ya jike da ruwan sama, a lokacin sukayi sallama su duka suka shigo, nayi mamakin ganin wannan bakuntar dukda dai awurina babu bako acikinsu. Muka tarbesu yadda yadace. Bayan mungama gaisawa alhaji yafadi abnda yake tafe dasu, munyi mamakin wannan ikon Allah, ananne alhaji ya labarta mamu kamar yadda umma ta labartamamu a baya... Munyi farin ciki marar misaltuwa a wannan lokacin, idan natsaya fadar komai zamu bata lokaci. Hawayen dasuka rinka zubowa daga idanun alhaji yasa hajia bnta tambayarshi dalili bayan abnda yaketa mafarki yafaru, ya samu abnda yafidda rai dashi a duniya ('yan'uwa), "ba komai nake tunawa ba sai bilkisu" alhaji yafada yana kuka, "dukda dai ba ciki daya muka fito da itaba ai mahaifinmu daya baikamata tayi hakaba, bilki ta cuci kanta, yanzu ni kadai..." Kuka yaci karfinshi batareda ya ida maganarsa ba. nanfa aka shiga bashi hakuri dole yatausasa zuciyarsa. Aranar alhaji ya mallakaman yasmeen, kuma yanemi alfarmar a aurama usman hadiza kanwata, umma batayi musu ba, saimadai tace "ai 'ya'yanka ne gasunan duk yadda kayi shine dai dai". Can na hangosu sunayima junansu wani irin kallo suna murmushi, basusan na dade da gano abnda ke tsakaninsu ba tunda dadewa... Ranar kau murna har ta bayan kunne, muna cikin wann halin sai haleematu takirani, ina dagawa tafadamun gatanan kofar gida, cikin murna nafita domin inyimata albishir, kuma inji ita wane mijin ta samo.. Su biyu nagani a kofar gidanmu ko wacce tana tsaye agabn motarta, kowace taci kwalliya tayi kyau sosai idan natsaya fada zamu cinye lokacin anan. Barista sady ce da haleematu usman zango... Ananfa suka daureman kai akan abnda sukazo man dashi sbd dukkansu sunzoman da maganar aure ne kuma babu wadda zata zauna da kishiya, barista ta gama komai har gidan dazamu zauna ta shirya kuma ta shaidama iyayenta, haleematu kuma nine ta fiddo a matsayin wanda take so sabanin zabin iyayenta kuma yauce rana takarshe dasuka bata cikin kwanaki biyar. Lokaci guda nafara tinanin halaccin dakowannensu tayiman a rayuwa, nanda nan wasu kalmomi suka rinka yawo acikin kaina "kada kadamu nima wata rana zan iya zuwa agurinka neman taimako!!!" Wata hajijiya tafara daukata ina juyawa sai naga yasmeen tsaye abayana tanata zubarda hawaye.... [12:02AM, 24/09/2016] ✨@lh@ji✨: 38ALKAWARI Part 38(Karshe) Su biyu nagani a kofar gidanmu ko wacce tana tsaye agabn motarta, kowace taci kwalliya tayi kyau sosai idan natsaya fada zamu cinye lokacin anan. Barista sady ce da haleematu usman zango... Ananfa suka daureman kai akan abnda sukazo man dashi, sbd bantaba tunanin dayansu zata fuskanceni da maganar soyayya ba, sai gashi lokaci guda dukkansu sun bijiroman da maganar aure kuma babu wadda zata zauna da kishiya acikinsu... barista sady ta gama komai na aurenmu har gidan dazamu zauna ta shirya kuma ta shaidama iyayenta... Haleematu kuma nine ta fiddo a matsayin wanda take so sabanin zabin iyayenta kuma yauce rana takarshe dasuka bata cikin kwanaki biyar tafiddo wanda takeso kokuma su bata wanda ransu yakeso. Lokaci guda nafara tinanin halaccin da kowannensu tayiman a rayuwa, nanda nan wasu kalmomi suka rinka yawo acikin kaina "kada kadamu nima wata rana zan iya zuwa agurinka neman taimako!!!", tabbas komai ba mai wahala bane awurin Allah (S.W.A). Wata hajijiya tafara daukata ina juyawa sai naga yasmeen tsaye abayana, ina hada ido biyu da ita natuna da maganar da doctor yafada: "dole asama mata farin ciki arayuwa kuma aguji sanyamata bakin ciki ko bacin rai indai anason lafiyarta"... Gaskiya inason yasmeen sosai kuma bazanso inyi silar raunana wani bangare na rayuwarta ba, nafada acikin zuciyata, ko bakina baisan da maganarba balle mutanen dake kallona... Lokaci guda kuma namaida dubana akan yan matan guda biyu kowacce ta hade fuska kamar basusan ko minene fara'a ba balle ayi maganar murmushi. Cikin kasala da rashin kwarin gwuiwa na nufesu kafafuwana na kyarma ina tafiya kamar dan koyo mai tafiyar ta ta ta, dakyar na iya tsayawa agabansu nayimasu bayanin duk abinda ke faruwa kuma na shaida masu har anmallaka min yasmeen wadda take masoyiya kuma yar'uwa tajini aguri na sbd haka aurena da ita yana nan tafe batareda jimawa ba. Rufe bakina keda wuya haleematu tajuya a fusace tanufi motarta, bayanta nabi dasauri ina kiran sunanta Haleematu! Haleematu!! Amman ko kallona batayiba balle ta amsa kiran danakeyi mata, afusace tabude motarta tareda kargama mata key "haba haleematu dan Allah kisaurareni, yaya zamuyi irin wannan rabuwar", ko kallona batayiba, ta fizgi motarta tayi gaba. Nayi bakin cikin irin wannan rabuwa damukayi. Ahaka najuyo agun inda nabar barista tsaye domin ganin ita ya tamu zata kare, amman naduba sama ko kasa babu barista sady saidai sawun tayar motarta, alamar itama tabar wurin... "me yasa zakabarsu su tafi, na yadda ka auresu", sama sama naji maganar tana shiga kunne na shiyasa nayi saurin juyowa domin tabbatar da abnda kunne na yakeji, "na yadda ka auremu mu duka", haba yasmeen kinsan zuciyata dake kadai takudurci zama har karshen rayuwa ta, bazan taba yimaki kishiya ba ta yaya kike kokarin sanyani abnda bazai yiwuba, ina gama magana nawuce zan koma cikin gida, ita kau ko motsawa batayi ba, "kitaho mushiga ciki mana" nafada tareda juyowa agareta, "bazan taba barin wurinnan ba harsai ka nemosu" tafada tareda dauke fuskarta daga gareni, dakyar nasamu na shawo kanta muka koma cikin gida tareda alkawarin na yadda zan auresu gaba daya. Bayan munshiga gida sai ga haleematu ta dawo, har cikin gida ta fadamun ta yadda zata aureni ahaka zata zauna da kishiya. Bamu dauki wani lokaci ba sai ga barista sady itama ta shigo tareda fadar itama ta yadda in auresu gaba daya. Murna kau awannan ranar abin ba acewa komai. Nan muka daidaita kanmu iyaye suka shiga ciki akayi duk abinda yadace. Aka tsaida ranar aurenmu tareda na su usman lokaci guda akayi komai. alhaji jafar ne yadauki nauyin komai kuma ya hana iyayen kowane bangare yin wani abinda yashafi bikin, hatta kayan daki shi yayima kowace amarya kuma ya mallaka mana gidan dazamu zauna. Lokaci yazo akayi biki cikin farin ciki akasha shagali. ALHAMDULLAH Anan labarinmu ya kare, sai kuma wani lokaci in Allah ya sake hadamu

Shin Ana Bukatan Blog ko website Kamar wannan kodai kamar Shafin Duniyan Fasaha, za'a iya samu a kan farashi mai rahusa daga Babban kanfanin Be With Me Technology Yola, Wayanda suka kware wajen Website Design da kuma hada Mahajar Waya. Za'a iya tuntubansu anan ko a wannan layin +2349039016969

Get Professional Website Design For your business Today Here. You can also visit our Tech Blog for more awesome Information. 
adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *