Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Thursday, February 2, 2017

Etrat complete

adsense here

🍃ETRAT🍃 Complete By Hauwa jabo 08:06 No comments [5/16, 1:10 PM] Auntie M. Jabonation✍🏾: 🍃ETRAT🍃 1&2 Na Hauwa M Jabo Zaune nake a kan daya daga cikin manya- manyan kujerun da suka mamaye falona, wanda dagani kasan cewa gidan akwai ni'ima da hutu mara iyaka a cikinsa, ga wadata ta kowane fanni amma kana dubin mai gidan, wato ni zaka fuskanchi cewa ina cikin matsananciyar damuwa... Tunani nakeyi wane irin haline nasamu kaina a ciki? wanda nikaina nakasa gane bakin zaren abun!! nidai sunana ETRAT, mahaifina yanada hali dai-dai gwargwado tayanda zamu rufawa kanmu asiri. Inada k'ani guda daya Hammad, da yar autarmu Iffat, atak'aice nice firs born a gidanmu, nayi karatu daga prmry har zuwa secndy, bayan na kammala secondry, nanfa mahaifina yace dole aure zaimun, araina nakance naga yanda ake aure ba miji. Allah yayi min kira ta halitta, wacce duk namijin da ya kalleni nasan sai ya maimaita, ni ba doguwaba kuma ba gajeraba, inada matsakaicin tsawo gani yar duma duma dani, inada hips sosai wanda har asibiti naje inason su bani magani su rage girma, akace ba magani saidai ayimin aiki arage su, ana zaune k'alau ina naga kud'in ragiyar hips? Tun daga nan ban k'ara zuwa asibiti zancen ragiyar hips ba, kirjina cike fam, kamar an girkasu gasu lukuta-lukuta, inada ido manya manya wayanda idan ka kalleka sai ka kauce, dan wai sexy ne injisu, wasu na cewa kamar nayi sha haka nake yi da idanuwana, abin yazamomin kamar al'ada lumshesun da nakeyi, amma ana cewa wai dagangan nakeyi, hancina dai dai ni, kai nidai badan kar inyi saboba, da sai nace ni dai na cika goman da ake cewa mutum dan tarane, sabida banida rangwame ko daya a halittar jikina, fagen gashi kuwa, nikaina bansan inda nayi gadon gashiba, sabida mamata da babana dukansu hausawan sokotone gaba da baya, haka Allah ya halicceni da gashi bak'i silk ga tsawo ga shegi ni farace amma ba irin mugun farinnan ba ataqaice dai wllhy inada kew sosai, wata baiwa da Allah yamun itace kwata- kwata bana warin zufa, kuma idan nasaka turare ajikina ko bashida tsada zakiga yadade ajikina bai bi iskaba, wanda hakan yakesaka bana saka turare sosai . Sai kiji ana "wane turare kika saka haka Eetrat??" basusan cewa jikinane keda wannan baiwarba, kuma gani da wata irin mahaukaciyar tsafta, ga k'yank'yami da yake damuna, idan guri bashida tsafta komi tsaftar abinchin sa, bazan iya chiba, ni kuma haka allah yayini.... Arayuwa na tsani samari, burina in auri tsoho mai shekaru masu yawa, atunanina yafi sanin darajar mace, bantaba kawo zancen saurayi arayuwataba, wanda har nakai shekara 18 amma ba wani dattijo dayazo neman aurena, duk samarine, hakan yakan bani haushi da takaici narasa miyasa wayanda nakeso basa sona, sai wani sarkin nachi waishi Mahbuob, shinefa yake biye dani baya barin kowa magana dani kuma shi bayamun magana, atunaninsa zansoshi baisan ni sai dattijo ba, nifa ko sa'ar babane ashirye nake da na aureshi. Mahbuob matashine dan kimanin shekara 29, Wanda ya kammala karatunsa, mahaifinsa yasamamasa aiki a airport, duk sati sai yazo gidansu gun iyayensa, ya gaidasu haka zaizo gun babana suyita tadi, har sai ya ganni sannan yatafi gidansu. Bai taba furtamin yanasonaba, kuma baigayawa mahaifinaba, amma duk unguwarmu kowa yasan cewa yanasona, wasu har matar Mahbuob suke cemin, ni kuma ko a jikina, dan nikam ko za'a mutu sai dattijo wanda yasan darajar mace...... 🍃ETRAT 🍃3-4 Na Hauwa M. Jabo Idan Mahbuub yazo, sai ya rabawa yaran unguwar kud, da kayan kwadayi, yace musu duk wanda sukaga ya min magana to sugayamishi, haka kuwa sukeyi, suna kai masa rahoton duk wani motsina, idan aka gaya masa wani yamin magana, zai nemi mutumin yamishi magana da lalama, yace yayi hak'uri wannan matarsace, yadaina yi mata magana, idan kuwa yagamaka bakajiba aka k'ara gayamasa kazo, to zai saka yaransa suyita jifanshi sai ya daina kulani, hakan yasa samarin gabaki daya suka daina zuwa gurina, nadawo banida kowa ba tsoho ba yaro, kuma shi Mahbuub din yak'i fitowa yayi maganar aurena.. Ranar wata assabar Mahbuub yazo gurin baba suna tad'i kamar yadda suka saba duk sati idan yazo hutu gida, yakanzo gurin baba, yauma haka nikuma nadawo daga islamiya kenan ina shiga gida sai Mahbuub yamike yace' "ni zan tafi baba" ashe duk yazo haka yakeyi, ina dawowa daga islamiya daya ganni sai yatashi yak'ara gaba, sai kuwa baba yace mishi "zauna inada magana dakai" ya zauna baba yace mishi "Wai miyasa Eetrat na dawowa daga makaranta, duk muhimmanchin maganar da muke, sai ka katseta, katashi katafi?? ko itace agogonka??" Mahbuub ya sosa k'eyya azuciyarsa yace ashe har anganoshi!! "Aa'aa baba, kawai ina tunanin yarane sun dawo gida, zaka shiga gida kuyi tadi da iyalinka, shiyasa, wai kar na shiga hak'k'in ka dana iyalinka," sai baba yace, "Idan dai wannan ne to kayi zamanka bana shiga gida sai dab da magrib idan zanyi alwalal sallar magrib" yace "to baba" suna tsaka da tadi sai aka kira baba awaya yadan tashi yakoma gefe yana magana, Mahbuub haka yazauna sai ga iffat qanwata aguje an biyota, Eetrat ce ta biyota, wai ta yaga mata littafine ai kuwa iffat tayi jikin Mahbuub, Eetrat tabita Mahbuub ya riqe hannun Eetrat yana bata haquri, haka yaji wani yarr a jikinsa, sai lokacin Eetrat ta tuna cewa ba dan kwali akanta balle takalmi, kuma kayan jikintama sai ahankali, nan take kunya takamata, tajuya zata shiga gida aikuwa yak'i sakin hannunta, tajoyo ta mashi kallon na huqura zan shiga gidane. Tawani lumshe ido, bashiri ya saketa sabida yanda tayi da ido ya firgitashi ,nan fa baba yadawo yana tambayar lafiya, iffat zatayi magana kenan sai Mahbuub yace taje gida, shi yagayawa baba abinda ya faru baba yay dariya yace, "Ai haka iffat take da tsokana kamar me, Eetrat, din ma takusa aure naga wazata tsokana..!" ba shiri Mahbuub ya mik'e tsaye yace "WHAT!!!???" Baba yace "lafiya kamar nagaymaka mutuwa" Sai lokacin mahbuub yadawo hayyachinsa yaga ashe har tsaye ya tashi, tuni kunya takamashi, ammfa idonshi sunyi tsuru-tsuru (kamar Jabo batada kud'i) baba yaso yagane cewa Mahbuub, Eetrat yakeso, amma baice komaiba, tunda yayi kusan shekara yana zuwa guri na baitaba gayamun ba, nandai baba yakawar da zancen azuciyansa, har aka fara kiran sallaar Magreeb, suka nufi masallaci dan gabatarda farali, amma fa hankalin mahbuub kwata kwata baya tare dashi.....zan chi gaba 🍃ETRAT 🍃5&6 Na Hauwa M. Jabo Yana sallah amma kwata -kwata hankalinsa baya tare dashi, dan kuwa da ace shi kadai yake sallan sai yayi demuwa fiye da goma, ba abinda yake mishi yawo akai sai lafazinda baba ya gayamasa ai "ETRAT TAKUSA AURE" nan yatuna da hannunta da yakama wani laushine dashi kaman auduga ga wani k'amshin turare dayaji tanayi wanda baitaba jin irin saba, idan na aureta na more gaskiya ina sonta, kai yau zan gayamata abinda ke zuciyana, haka yayita saqe-saqe a sallah nan take yace astaqfirullah..!!! miyasa baituna da wayannan abubuwaba sai yanzu, take yatuna ashe sallah akeyi yayi istiqfari yadawo hayyachinsa, yayita jiran liman yace allahu akbar yadago, daga sujada yaji shiru, ashe anqare sallah yanachan yana tunani, da ya gaji sai ya dago kai, koda ya duba sai yaga wasu har sun watse daga masallaci, yaduba yaga baba na lazimi kunyar duniya ta isheshi baisan lokacinda aka qare sallah ba, yanata tunani yadai san anyi raka'ar farko dashi sauran kuwa sai Allah. ya sallame yaje gun baba yace mishi zai tafi gida baba yace "bakada lafiya ne" yace " lafiya na k'alau baba" "To amma naga lokaci daya ka chanza" yace "lafiyata lau baba idan nayi sallah haka nake "(kaji bawan Allah) bayan kuwa firgichin jin za'ayiwa Etrat aurene, baba ya yarda da abinda yace sukayi sallama yatafi gida... Etrat kuwa kunya ta isheta yau namiji yaganta ba hijabi, har ya rik'emata hannu wanda tun tana karama take zunbula hijabi, har data girma, sabida mazaunanta dasuke motsawa da kansu idan tana tafiya sai tak'ara saba saka hijabin har yazamo mata al'ada, yau shine namiji yaganta har ya riqke mata hannu kuma tarasa dalili idan ta tuna sai tayi murmushi maimakon ta tsaneshi, baba yashigo gida sai taji tanason taji labarin Mahbuub agurinsa, amma kunya takeji, wata zuciya nacewa tambaya wata nacewa aah haka har sukaje chin abinchi dare, sai ga Hammad yashigo yace " baba wai Mahbuub yana magana" mamaki ya cikawa baba ciki yanzu fa suka rabu ko yayi mantuwane? haka dai da waswasi ya fita ita kuwa Eetrat ji take kamar ta lek'a taganshi tadawo, karo na farko arayuwanta dataji cewa zata iya auren yaro idan dai Mahbuub ne, dan ya burgeta.... "Lafiya dai Mahbuub?" . firgigit yadawo yace "lafiya lau naje gidane wai sun dauka bazan dawoba, shine basu ijiyemin abinchiba, shine nazo nan kamin achinye inchi na iffat, sai Eetrat tadafa mata wani." Baba yay murmushi yace to bismillah shigo.. babana dduk yanda kake dashi baya kawoka cikin gida, iyakachinku gofar gida, ko zaure amma Mahbuub dan gatan baba har cikin falon baba, dama duk tare muke chin abinchi dadare, anachi ana tadi bansan cewa yashigoba da sai na zunbula hijabi, amma ina saida nakawo tsakiyar falo naganshi suna chin abinchi da baba da iffat, dama naje kawo ruwa ne lokacin da ya shigo, kunya takamani gani dagani sai wata riga mai kamar bes sai wani shot nika, na rasa yanda zanyi bazan iya komawa ba, natsaya chus sai Hammad yace "Aunty kishogo mana." kamar an mini allura na zabura sai nawayance nace "Yau baqo mukayi?" iffat tace "Eeh, yaya Mahbuub ne" nashigo na zauna, bai dago kai ya kalleniba sannu kawai yacemin haka yasa na sake nachi abinchina, amma inata sake sake araina, nace dama karya yakeyi yakoramin samari amma gashi ko kallo ban isheshiba, kuma yaqi cewa yana sona, lokaci daya naji na tsaneshi kaman da.. Dago idon da zanyi in harareshi sai kawai muka hada ido, sai naga yay murmushi bansan lokachinda nima nay murmushiba, nakawar da kai take naji na k'oshi .....zanchi mana gaba type wahala wllhy [5/16, 1:28 PM] Auntie M. Jabonation✍🏾: 🍃 ETRAT 🍃 7&8 Na Hauwa M. Jabo Namike tsam zan tashi, mama tace "ina zaki?" nace "nagoshi " zatayi magana nayi mata wani iri da ido.. Ta tabe bakii batace komaiba, ina tashi shima yaji ya k'oshi haka dai dan kar agane ya rink'a tusawa, har suka kare, yayi godiya yakara gaba, yaso ya fadi abinda ke zuciyarshi, amma sai ya kasa ya haqura yatafi, ita kuwa Eetrat duk kunya ta isheta namiji yaganta wit out hijab...! Tun da safee sukaji sallamar bak'uwa ikon Allah!!! "Yau maman Ameer kece a gari!!!" haka tace "wllhy nice" "Saukan yaushe?" tace yau satinsu biyu da da dawowa " kishigo daga chiki mana" murna gurin mama ba'a magana yau babbar aminiyarta ta dawo, "Bari inje in hada miki abin karyawa" maman Ameer tashiga d'aki, Maman iffat ne ta hada mata break fast dai dai aljihunsu, sunachi suna tadi maman Ameer k'awar Maman iffat ne sosai, wanda tun suna yan mata tare suke, da suka girma kowa tay aure ta kama gabanta, amma suna zumunchi sosai sai wannan tafiyar da sukayi Lebanon basu dawoba sai bayan shekara 7, sunyi missing din juna ba kadan ba, suna ta tadi bayan rabo nannefa maman Ameer tace "Ina Eetrat da hammad" . "Wallahy duk suna barchi ne, Kinsan yau Sunday ba skull," batamasan iffat ba wacce bata nan mama ta haifeta, sunsha labari sosai, chan saiga Eetrat ta taso daga bacci guraren qarfe goma na safee, Bayan tayi brush ta wanke fuska, taje zata gaida mamarta, ta tarar da bak'uuwa, ta dan ganeta, ta gaidata, suka gaisa bayan ta fita mamaki ya kamata, wannan Etrat ce ta girma haka koda nabarta shekaranta goma sha daya fa, mama tay dariya duniya kenan gatanan sai aure, nan maman Ameer ta gyara zama tace "An tsayar mata da miji ne" mama tacee " aah" nan maman Ameer ta kwashe da dariya suka tafa, tace "wllhy haka na riqa jin inzo giddannan akwai alkhairi, kamar Ana korani, haka na rik'a ji, shiyasa na danno sammako, ashe etrat rabon Ameer ce.." . batasan randa ta rangada gudaba dan murna, muka shigo da gudu muma muji, Mama ta hararemu muka koma, Maman Ameer ta kirani nazo taqara kallona sama da qasa ta qara rangada guda, tace "Anyi angama kuma wllhy tayi" ni bangane komaiba Mama tace "Jeki ki hada muku abin karyawa" natafi chike da mamaki mama da maman Ameer suka kitse magana akan za'a hadani aure da Ameer Hussein, tuni baba ya amince sabida yasan iyayen sa suna da kirki sosai, kuma yasan barewa bazatayi gudu d'anta yayi rarrafeba.. Da maman ameer zata fi tace muzo muyi hoton tarihi aka dauki hotuna kala kala tanata murna nidai ba ace mun komai ba, kuma ban kuma tambayaba amma naga kowa cike da murna da farin ciki, bama kamar maman Ameer ba duk inda nayi idonta akaina, suka rabu da mama chike da shauqin junansu. babansu Ameer Hussain mai kudin gaskene sosai, wanda yake sana'ar saida gwalagwalai a Beirut babban city na qasar Lebanon, Ameer hussain shi kadai yake agurin iyayenshi, mamanshi saida ta haifi yara guda 8 bayan Ameer Hussein duk suna rasuwa sai ameer hussaini ya rayu, kuma shine babba, yasamu tarbiya sosai agurin iyayensa wanda aga bansu ya tashi sai dai kash ameer Hussein ......zan chi gaba idan nay sallah☺☺ [5/16, 2:22 PM] Auntie M. Jabonation✍🏾: 🍃ETRAT🍃 9&10 Na Hauwa M. Jabo Kash Ameer Hussein mushkiline har na bala'ee, wanda ko magana idan yayi zaki iya lissafa haruffa nawa ne amaganar tashi, fuskarshi adaure take, baya shiga harkar kowa sai ta gabanshi, kai ko dariya bayayi sai murmushi, shima wa iyayensa yakeyi awajee baya ko murmushin, duk wanda yayiwa murmushi to yagodewa allah.. Tun yanada shekara 8 aka kaishi qasar Cyprus karatu inda kowa yasan k'asar akwai tsadar rayuwa, sabida kasar da sunsan yanda zasuyi ko numfashi idan kayi sai ka biya su, haka komai tsada a qasar ammafa qasar kaje kagani ta hadu sosai wllhy... Anan ya girma gurin wani abokon babanshi, yayi prmry yayi secondary har yashiga AUM babbar jamiar gasar ce, anan yayi karatun shi har yayi mastered dinshi, dayake allah yayishi mai hazak'a sai yayi saurin kammala karuntunshi yana da shekara 31... Ameer Hussein ba abinda yatsana arayuwarshi kamar mace, bai taba daukar mace a matsayin Abu mai darajaba, Sam batada daraja, haka yake ganinsu kamar bayi, sai yazamo kwata-kwata bayason mace ko abokiya mace baitaba yiba balle yayi tunanin aure, ikon Allah Ameer Hussain dai ya tsani mata wllhy.... Shidai kawai karatu, skull mate, course mate, musulmai, da arna farare da bak'ak'a, son nuna mishi k'auna, amma baitaba amincewa da ko dayaba, karkuyi tunanin ko mace ta taba yimasa wani abu aah..!! Wanda yasa ya tsani mata, ko d'aya, kawai ya tsani matane arayuwansa. h Haka ya k'are karatunsa ya dawo gun iyayensa, Lebanon yay shekara biyu dasu achan, har suka dawo gida Nigeria sokoto. Ameer Hussein kullum bashida aiki sai danne danbe da Ipad d'insa, wacce inajin tafi mace muhimmanchi agurinsa, shidai haka rayuwarsa take kuma baya shiga harkar kowa kuma bayason ashiga tashi... Sai dai matsalanshi daya akwai k'azanta da take damunsa, bawai ta tufafiba aah. ta gurin zama idan kahadu dashi ahanya yana k'amshi bazakayi tunanin zai kwana a inda yake kwanaba, dan hargisti da yamutsewar gurin wannan akan wannan wancan akan wannan.. tofa kunji tsabtar tsula inji ba sakwakwace..... ** ** ** ** ** ** ** ** ** ** ** Maman ameer tadawo gida cike da farin ciki da murnar tayiwa Ameer d'inta mata, tasamu alhaji labbo mahaifin Ameer tagayamasa, yaji dad'i sosai musamman dayaji cewa yarinyar yar gidan wayee, kuma dama bayason yar boko wacce tayi zurfi da karatu yafison yar daidai wacce zata iya hak'uri da Ameer hussein, Maman Ameer tanuna masa hotunan da suka dauka tare da Eetrat, nanfa alhaji labbo yaqara jin dadi da samun suruka kyakyawa kamar Eetrat. murna agurinsu ba'a magana, yinin ranar gaba daya magana daya akeyi, ya auren zai kasance, suna jiran sarkin mishkilan duniya yazo sugayamishi suji abinda zaice, sunsan sai sunyi dagyar amma kuma zai amince duk da hakan. Bayan sallar esha sukaji karar matarshi yadawo daga office yana tafe yana danna iPad a hannu har yana karo da fridge a fallo sannan yadaga kai yay murmushi...(laaaaa dama maza sunada dimple ne??) Ammafa wllhy Ameer hussain hadadden guy ne ta kowane janibi babanshi sak ya biyo, saidai shi black ne amma yanada haske kamar irin black American dinnan haka yake. Gashinshi Wanda ya kwanta lub akanshi, haka gashin yake ko ina ajikinshi musamman a qirjinsa gashida faffadan qirji atak'aice dai Ameer Hussein yakai iya inda namiji yake kaiwa sai dai mishkilanchinsa yayi yawa..... "Sannu umma sannu abbah" haka yagaida iyayensa yana murmushi yazo yayi musu kiss a fuska al ada dai ta turawa, zai wuce daki Alhaji abbanshi ya kirashi yadawo ya zauna, ananfa abbah yafara yi mishi maganar aure ya bushe da dariya budan bakiin da zaiyi sai yace..... 🍃ETRAT🍃 11-14 Na Hauwa M. Jabo "Wallahi abba kuna bani dariya da mamaki, ni mizanyi da mace???" ya wani ya tsina fuska irin maganar da ake mishi sam batada muhimmanchi a gurinsa.. abba yaci gaba da magana, "nidai dan Allah bamuce kaje ka nemo mataba ga wannan yarinyar mamanka ta nema maka, sai ka aureta," Abbah dai yayi iya k'ok'arrinshi na fahimtar da Ameer amma yak'i fahimtuwa, nanfa Umma ta daka mishi tsawa tuni ya natsu, ba shiri Ameer hussain ya amince, nanfa suka fara murna Umma taso yaga pic din Eetrat amma ina yak'ara gaba abinshi, Umma takamoshi ta rungumeshi tana saka masa albarka tana murna........ Mahbuub daren nan kasa bacchi yayi dagyar yasamu yayi bacci gashi gobe sunada buki a famly d'insu kuma dole yazamana yananan sabida haka bazai samu yazo gidansu Eetrat ba haka yayi juyayinsa, Monday yakoma aikinsa yamatsu sati ya zaqayo a yazo kawai ya gabatarda kansa a gurin Eetrat.... Nimq kuwa daren haka nayi tafama da tunani na rasa miyake damuna nida nake bacci qarfe 9 na dare yau gani har kusan asuba ko gezau, kuma narasa gane mi ya hanani bacci, dak'yar nasamu nayi baccin sai mafarkin Mahbuub, anan nagane cewa fa guy din ya shiga rainane amma ba yanda zanayi tunda baya sona, fadawa duniya kawai yayi. D safee naso nayi tadinsa a gida sai mukayi bak'uwa Maman Ameer wacce tasa namanta da Mahbuub, koda yake ni bansan zancen Ameer Hussein ba kwata-kwata tunda bawanda yagayamin su biyu sukayi shawaransu basu gayaminba.... Nidai araina nagane cewa inason Mahbuub amma kuma ina jin tsoron yanda naga yazo gidammu ko kallona baiyiba, kuma ya bazawa duniya cewa yana sona ni banga so annanba, naga kullum Umma da mama sai sunyi waya idan tana wayar sai ta koremu karmuji mitake cewa, dai dai da rana daya bankawo cewa maganar aurena sukeyiba, nikuwa gashi sai begen Mahbuub nake a zuciyana.... Ranar assabar kamar kullum Mahbuub yazo gun baba sun fara firarsu da suka saba baba yadauki mahbuub abokin shawaranshi sabida yanada hankali sosan gaske suna magana sai baba yace mishi "Mahbuub inason muyi wata magana nae" yaji dadi yadauka baba ya gane yanason Eetrat ne yasosa qeya yace " inaji baba!," " dama maganar auren qanwarkane ya matso..." "Ina zuwa baba wace qanwar tawa?" baba yay murmushi yace "Eetrat mana" " ETRAT baba?" kikaji..... Kikaji shiru lokaci daya, Mahbuub ya fashe da kuka baba yana lafiya mahbuub?? yay shiru yasake fashewa da kuka baba yarasa gane miyake faruwa sai tambaya yake amma ba amsa sai yanzu Mahbuub yagane kuskurensa na k'in furtawa Etrat kalmarr SO... sai kawai duniya ya fadawa maimakon wacce yakeson yagayamata amma yak'i fada, wauta yayi? ko hauka? ko ma miye Dai yayi danasanin aikata wannan wautar. baba yana tambayar sa nanne dai Mahbuub ya fayyacewa baba abinda ke cikin zuciyarsa... Baba yay shiru ko ba komai Mahbuub yanada kirki kuma iyayensa masu mutunchine ,amma kuma yaza'ay ya warware Alk'awarin da yayi, gashi har ankusa saka rana, baba ya tausayawa Mahbuub, amma ba yanda ya iya, Ya dubi Mahbuub yace "Miyasa baka fadaba Mahbuub?" yace "sabida ba matana bane, da Etrat matanane da tun lokachinda nake fama da sonta na furtamata amma sai na ijiye abun araina wannda yanzu nagane hikimar Allah ta rashi furtawan..." haka dai Mahbuub yatafi da jimamin rashin samun biyan buk'atarsa, amma fa yanason Etrat sosai, kuma yana kishi da duk mijin da zai aureta.. baba yashiga gida yafadawa Mama abinda yafaru, Mama tayi jimami sosai, kuma ta tausayamasa ana maganar sai na shigo naji abinda suke fada bance komaiba, amma banji zancen wai an mini wani mijinba, na dauka Baba yabi ra'ayinane na sai tsoho, amma kuma baba baisan inason mahbuub ba ??gaskiya nidai da anmishi magana ace ya turo haka naita sak'e- sak'e araina, har suka tafi suka barni, bansan sun tafiba..... ashe so yakan hana bacci zancen da na rik'a yi Kenan a zuciyanta, amma fa naji haushin hukunchinda Baba yayanke batareda ya tambayeniba, haka na hak'ura amma fa abun na rain....... Ameer Hussein har ya manta da zancen wata yarinya wacce ko sunanta baisaniba, kuma bayama son yasan sunanta, Umma ce tashigo da fara'arta tasamu Ameer yanata game a iPad d'insa, Umma taje kusa dashi tazauna yay murmushi " sannu umma.!" tace yauwa tay shiru chan tafara magana "dama zancen Etrat ne, shine muka yanke shawaran gobe lahadi da k'arfe goma na safee zamuje kagaida iyayen rarinyar, kai kuma sai Ku gaisa da yarinyar." baice komaiba kuma baidago kai ya kalletaba tace "kanaji na kuwa?" yace "Eh Umma Allah yakaimu, goben" tayi mamakin amsar dayabata, amma sai tashare tasaka mishi albarka tak'ara gaba, yaci gaba da danna iPad d'insa, Umma takira Mama tagayamata gobe zasuzo harda Ameer, Mama tay murna sosai tagayawa Baba aka fara shirye shirye, nidai kawai ancemini zasuyi bak'i amma bansan gurinaza'azoba, andai kawo mani sababbin d'inki wani material less ne ,akayi dinki mai kew wanda dagani zai kamani sai wata qaramar sarqa mai kew nidau sai kallonsu kakeyi......bari in fito wanka zan chi gaba☺ [5/16, 3:09 PM] Auntie M. Jabonation✍🏾: 🍃ETRAT🍃 15-16 Na Hauwa M. Jabo Kallonsu nakeyi abun bai bani mamakiba sai da naji cewa wai harda Abban Ameer za'azo, to amma miye had'in zuwan abban ameer da bani sababbin dinki?? Haka dai na gaji da sak'e- sak'ena araina, kuma ban sami amsaba.... anyi aiki sosai wanda aka share gidan ko ina aka yi girki kala-kala nidai pizza kawai hada musu,da kuma shawarma drink wanda akeyi da shinkafa, kwakwa,da madara yanda na had'a shi, Bayan na jik'a farar shinkafa, sai kuma na d'ora daya akan wuta, ta dahu kamar tuwo, na sauketa ta hada da jikak'k'iyar shinkafar da kwa- kwa, na markad'e, na tace, na samu sugar da madara na saka, aka saka a fridge, gaskiya yay dadi sosai nima nasani, mun kammala duk wani abu na tarbar bak'i bak'inmu kawai muke jira...... "Wai ina Ameer yake ne" inji abba, Umma " yana ciki yana shiryawa" "OK mudan jirasi kinsan mutumin naki mishkiline," shiru kakejii har sukai minti goma zaune abba yace "bari indubasa ingayamasa yay sauri" bude qofan keda wuya sukaga ameer kwance yana shara bacci abin ya bashi mamaki sosai yaje gun Umma " dama baki gaya masa cewa karfe goma zamu tafiba.? tace "Wallahy nagayamasa" Abba yace "To ai kuwa yana chan yana bacci abinshi," Umma ta fusata da sauri ta miqe Abba yace "dakata malama lallabashi zakiyi sai yayi fushi muje muga yanda bamaso a gun.!" haka sukaje suka tasheshi cikin kulawa da wayo irin na manya aka lallabashi ya tashi dayaga ran mahaifansa ya bachi kawai hak'uri kawai sukayi suka share, sai yayi sauri shima ya fara shiri. kwata kwata Ameer yamanta da zancen zuwa gurin wata mata, aransa yay dariya (wai mata!) a tsanake ya shirya dan kar ya k'ara bata musu rai, abinda ya tsana kenan arayuwarsa ganin bachin ran mahaifansa abinda ya burgesu shine tufafinsa yasa na k'asarsa Nigeria, wanda rabonshi dasu tun sallar layya ai kuwa yafito tas dashi ya kafa hula yafesa turare yay kew abinshi ya dauki bakandamiyarshi wato iPad, Yafito cikin minti ashirin yak'ara basu hakuri, sunata mamaki, ko ya sauko ne, shi yay driving din mota har suka isa kofar rini unguwar mu..... Nayi wanka nasaka kayanda aka kawomin, dama ni ba ma'abociyar kwalliya bace amma kayan sun fitar dani sosai, ga qaramar sarqan nan da na saka haka dai nafito kaman wata amarya, mazau nan nan nawa kuwa sun fito tsab atakaice dai nayi kew sosai nikaina naji haka ajikina..... Misalin qarfe 11 da rabi bak'inmu suka iso, Umma tashigo ciki su Abba da Ameer suka wuce sashen Abba, nanfa su Umma da Mama suka fara tad'i abinsu, ni kuma na fita na basu guri, zuwa 12 akace afito aci abinci, nanfa aka kwasa akayi fallon Baba, aka bajee chan-chan na hango Ameer Hussein zaune amma kanshi ak'asa yana abinda yasaba da iPad d'insa, nidama bansanshi so banyi k'ok'arin gaisheshi ba, fuskar shi na gefe mu kuma muna waccan barayin Ameer baici komaiba sai pizzan dana had'a, da kuma shawarma drink, koda bansanshiba naji dad'in abinchina daya chi, kuma su kadai yachi aka k'are chin abinchi ayanda ya mik'e bai waigoba kawai gaba ya k'ara bandamu dasanin ko wayeba..na kashe kwanukan naje na kanke, mukaje sallah, na idar da sallah kenan ina lazimina dana saba sai kawai ga Iffat, "wai Auntie kije inji Mama" natashi naje tace insaka powder fuskana yayi wani iri na k'ara goga powder a fuskata nazo kije fallon abbanku kina da bak'o inji Mama. ETRAT 17&18 Nace "bak'o Mama?" tace "Eh kije yana jiranki" abin yabani mamaki ni ba saurayiba balle inyi tunanin ko yazo gurina ne, araina nace ko tsohon da nake nemane nasamu araina nace tab.!! Haka naje pallon babana. Ntarar da mutum zaune yana danna iPad, ko game yakeyi oho nay sallama ya amsamin batare da ya dago kai ya dubeniba, na kuwa sha hijabina abina, nazauna a dayar kujeran gefen sa daga yamma, yanda nazauna haka nake zaune kusan awa daya bai dago ya kalleniba haushi yakamani sosai wai wannan shine baqon nawa ko kuma yaya?? har zan mishi magana, sai kawai guntuwar sarautar mu ta mata ta motsa, kawai sai na share shi, ai kuwa haka muka share awa uku bai dago kai ya kalleniba ni kuma ban mishi maganaba sai danne danne yake da ipad, can sai ga Iffat a guje ta fada jikinshi, "Yaya Ameer wai akawo maka wani abu zakachi?" nan natuna dako ruwa ban bashiba ko shiyasa yak'o yimin magana? yay murmushi yace "Ya sunanki ?" tace "Iffat shunana" yaja kumatunta yana murmushi, nanne naga ikon Allah, dama maza suna da dimple ne sai yau nagani, yace ki kawo min ruwa idan akwai sauran pizza akawo min, ta tafi dagudu ya bita da murmushi ahakan ya sake duk'ar da kansa ya chi gaba da aikinsa, aka kawo masa pizza wacce na ijiyewa kainace sabida ban chiba, kuma na wahala gurin girkawa, haka ya chinye ta tass. ko mai bai rageba naso inchi pizzar nan amma wannan sarkin shurun ya chinye, na hak'ura dan dole, yana chinyewa naga ya mik'e ya wuce abinshi, ko sallama babu amma wannan mutum anya gurina yazo kuwa...? oho. nidai naje cikin gida nachi gaba da shirye shiyen abinchin dare haka dai bakinmu suka kammala abinda zasuyi akayi bankwana naji ana cewa 20 ga may din yayi, nace mi za ayi 20 may kuma,? nace koma miye yau dai 12 may ne zamu gani har suka tafi wanda akace bak'onane bai daga kai ya kalleniba. Nafito daga kitchen naji mama tana cema Baba "Anya niko aurennan baiyi kusaba 20 ga wannan watan, fa? ba fa wani shiri da muka yi ita kanta yarinyar bamu saniba ko tana sonshi.?" sai Abba yace "nasan Etrat zata soshi kincemunfa awansu sama da uku suna magana, idan kuwa bata sonshi bazasu shafe awa uku.suna maganaba!!" tabbbbbb........ [5/16, 3:40 PM] Auntie M. Jabonation✍🏾: 🍃ETRAT🍃 19-20 Na Hauwa M. Jabo Lallai abinda najiyo gaskiyane aure za'amun tabbb...!! da wannan mishkilin mutum wanda ko gaisuwa bai iyaba za'ahadani aure, naja baya nakoma d'aki na fashe da kuka, ni wllhy bana son wannan mutumin gara Mahbuub sau dubu akanshi, nifa gaskiya bana sonshi, dayar zuciyar ai kya bari har amiki maganar aure sannan ki ce bakya sonsa idan aka ganki kina kuka mi zakice? wato labal kikayi kikaji sirrin iyayenki ko? nan take nay shuru kar asirina ya tonu haka naje nakwanta.... Da safeee natashi bayan nayi break fast baba ya ce yanada magana dani, nan gabana yafadi nasan cewa maganarce, haka jiki ba k'wari naje pallon Baba natararda Mama agun fuskanta a sake, nazauna gefen Baba yay murmushi yace "Etrat matar tsoho... " sai naji kunya narufe fuskana da hannuwana Baba yay gyaran murya yace "dama dai maganar aurenkine ya matso, shine kuma mu munriga mun badake agurin yaron gidan alhaji labbo wato Ameer Hussein wanda kuka tattauna dashi jiya da yamma kuma ga dukkan alamu kun aminta da juna sabida mamarki tace kun kusa awa uku kuna magana wanda ya tabbatar mana da cewa kuna k'aunar juna, saidai jin ta bakinki ma yanada muhimmanchi" nanfa zuciyata bak'i k'irin araina nace wllhy Mahbuub nakeso ba wannan Ameer ba shirun da nayi naji Mama tana cewa.. "nagaya maka ta amince kawai sai ki fara sanar da qawayenki 20 may auren" araina nace nashiga uku bansan yanda zanyi da rayuwataba baba yace inje Allah yayi min albarka, jiki ba kwari na tashi naje daki sai sake sake nake, wai zanyi aure nan da sati daya Lallai ma, ahaka har bacci yay awon gaba dani harda mafarkin Mahbuub zaune acikin wani k'aramin dak'i yanata dariya nace mishi lafiya sai kawai ya rungumeni, nan take nafarka natina malamin islamiyan mu yace ,idan kay mafarkin kuka dariyane dariya kuma kuka, nace duk yanda akayi Mahbuub yana cikin wani hali nay mishi addua naci gaba da baccina....... Wasa wasa yaune daurin aurena inda tundaga kan wurin sarki, har bakin kofar rini anan unguwarmu mutanene ta ko ina, gaskiya naga jama'a rabon da naga taron jama'a irin haka tun auren ruqayyah da basasa shekara nawa da suka wuce sai aurena, ko ina zancen aurena ake yau andaura auren AMEER HUSSEIN & ETRAT Allah yasanya alkhairi ni kuwa duk wani tsimi da ake yiwa yarinya idan zatayi aure anmini shi, wanda kun dai san sokoto sarai basai na gayamukuba, yamma tayi aka daukeni aka kaini gidan mijina da yake nan GRA bayan kowa ya watse ba ango ba abokan ango chan sai naji an murda qofa......... ETRAT 21&22 Aka murza k'ofan sai Naji maganar maza amma wani yare suke, sai naji sun kwashe da dariya sai dayan yace "Inaga fa nanne" suka k'ara murda k'ofa suka shigo su bakwaine harshi cikon na takwas hudu fararen fata hudu kuma bak'ak'e yan uwanmu, fuskata na chikin hijab nace araina dama yasan zaizo shine ya bari saida qawayena suka ,tafi nay tsaki araina... suka fara surutansu wani da yare wani da English haka dai suka gama shi dama bakandamiyarshice a hannunsa wato iPad.. yana abinda ya saba sun k'are surutansu suka kawo abinda sukazo dashi suka tashi yay musu rakiya naji lokacinda ya rufe k'ofa amma sai kuma banji tsoronda akace anajiba aranar farko ko miyasa oho? ban kara ganinsaba har bacci yay awon gaba dani. Tofa gidan aure na nake yanzu gidan k'aton gaske sabida zai kai rabin kilo mtr ko wane bari hadda lanbune a gidan ga swimming pool agidan k'aton gaske ne, falon wani irin babba dashi, dakuna gasunan sunkai guda 10 kala kala abin dai sai wanda yagani, bazan iya tsayawa lissafawaba nidai ganinan aciki. Yau nake ganin ango gobe nake ganinsa shiru, nikuma ko za'a kasheni bansan haryar dakinsaba. nafito falo nafara yan lek'e lek'ena har na hango kitchen, nanfa nashiga na hada break fast amma ba ango ba labarinsa, saida na hada kwana sha daya sai dai inji k'arar mota da safe dakuma da yamma inji dawowar mota, amma bana sakashi a idona tun ina damuwa har na daina damuwa, Wata rana guraren 12 naji k'arae mota abin ya bani mamaki ya akai yadawo da wuri haka, koda bana ganinsa, amma nakan rage tsoro idan Naji cewa akwai mutum a gidan, sai kawai naji motsin mutane, na fito waje, na daga kai naga Umma da Abba da wata mata, nay musu sannu da zuwa na kawo musu abinchi, sabida kullum sai nay girki dashi na dare da narana, sai dai in baiwa masu gadi sabida ba chi yakeyiba yau kuwa iyayensa suka chinye abinchin. Hakadai mukay ta tad'i dasu har yamma, wannan matar zata koya min motane har in iya, naji dadi sosai dadi ya bani key din motar sabuwa ta zamani naji dadi ranar kamar me. hakadai muka hira dasu suka tafi. An bani waya, an kuma bani numbr sa idan inason abu nakan yi masa sms amma bai taba reply ba sai da nayi wata biyu aginnanan ban saka Ameer Hussain a idonaba, wannan wane irin aurene?? Ba miji nayi dana sanin aurensa inason fita sai dai ingayawa mamansa tagayamasa bantaba gigin fadawa kowa halinda nake cikiba ranar wata laraba natashi nayi duk abinda ya dace, niba miji ba sai kwalliya dan banida bambanchi da hauwa jabo. Nafito sai kawai nabi wata hanya wacce bantama bintaba, acikin gidana sai kuwa ga tarin key's a sakale a wani guri, nadauka na fara bud'e bud'e in bud'e wannan in bud'e wanchan, dakunane atsare duk sunyi k'ura ko ba komai tsabta tana da kew na gogesu na yini aiki aranar, nagama kenan sai naga wani labule ina dagawa sainaga... [5/16, 4:27 PM] Auntie M. Jabonation✍🏾: 🍃ETRAT🍃 23&24 Na Hauwa M. Jabo Sainaga wani falo a hargitse, wanda ga dukkan alamu akwai mutun aciki, sai dai yanzu bayanan haka na gyara fallon na share tas komai nai arranging d'insa, yadawo kamar sauran dakuna, sauran kuwa nace sai gobe dan nagaji na kulle dakunanan na dawo sassana, nayi wanka na saka wasu kaya gasunan dai, na fito tas tas dani sai dai ba miji, bayan nadanyi bacci sai naji motsin mutum abayana nay balaeen tsorata watana biyu da kwana hudu bantaba ganinsa ba sai yau, hasalima bamu taba hada ido dashiba sai yau, fuskarsa a daure yafara min balaee " keee !!! Waya aikeki dakina?? Wayace kitabin kaya?? Ke mahaukacciyar inace???" Tofa ranar farko da na fara hada ido da mijina wanda nake zamansa wata biyu da kwanaki... shima da masifa yafara min magana, Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun., haka kawai nace araina sai naga ya juya har yakai k'ofa yadawo ya wani jawomin gashin kaina wanda yasa nayi wata irin k'ara, sabida zafin danaji yamun magana da ido alamar idan kika k'ara sai naci ubanki ya wurgani nafada akan hannun kujera wanda naji zafi sosai bansan lokacinda hawaye suka zubominba, nay kukan dana sanin aikin dana aikata, waya aikeki, ke dadi miji hajiyan zabta, haka zuciyata ta mai mai tamin, gobema kik'ara! Nanfa wasu hawaye masu radadi suka zubomin, dan nikam nayi rashin sa'ar miji, arayuwa anya wannan yasan da zamana adunuyi ma kuwa?? Wannan kamar baisan miye aureba, haka nayi jinya ta kwana biyu har na warke, ranar haka najishi shida abokansa, da matar daya daga cikin abokan nasa sunata magana a fallo suna dariya ni kuwa ina bacci ihunsu ya tayar dani daga bacci, ina fitowa mukai ido biyu dashi abin mamaki say yay murmushi, wanda bantaba ganin irinsaba arayuwata, araina nace amma fa mijina ya had'u, sai dai ba kyan hali yace mun... "keee!! ga k'awanan namiki matar abokinace zata riga zuwa gidannan, sai kema kije gidanta," sai matar tace, "Bamaso ai kayi mai wuyar tunda ka kawoni gidanta, mu zamu shirya kammu," Dayan abokin yace min, "Hajiya amarya ana hutuwa, tin dazu mukazo yace kuna bacci bazai tayar dake ba." Nai Murmushi kawai. daga nanfa bai k'ara cewa komai ba, Nan mukaita labari da ita matar mai kirki da ita, khadija ana ce mata sista khadee. Na musu girki hadda Ameer Hussein ya bud'e ciki ya kwasa shima, munyi sabo da ita sosai har tana zolayata wai bawani bayani shine fa araina nace tabbb.!! ni ko mijin banagani balle zancen ciki haka dai muka rabu mukai musanyar numbr, gobe sai naga mijina yazo da safee ina break fast yazauna shima yaci abinda na girka, ya bani mamaki sosai jiya da bak'i sukazo dgyar yaci abincin, yana farawa kuwa sai naga duk yafi dukansu chi, yauma gashi yazo yana chin abinchina, abin ya burgeni koda baya ko daga kai ya kalleni, mun kwashe wata daya kullum gida yake chin abinchi, sai ranar da gangan naki girgi, da rana wanda yadawo don chin abinchi, tun bakin k'ofa ya hango table din wayam, ya lek'a kicin yaga wayam, sai yazauna fallo sabida yana balaeen jin yunwa, kuma yanzu baya iya chin abinchin ko ina sai na gida, nafito kena sai nagansa zaune ko kallonsa banyiba, na wuce kitchen nahada tea mai kauri nazo d'ayar kujerar nazauna, yana kallon wani film da wani yare ,wanda bansan mi suke cewaba. Haka nazauna ina kallo nima, ina kurba tea na a hankali lokachi daya wani haushina ya kamashi.. ya zanzo gabanshi in zauna ina chin abinchi shi ko tea din inkawo mishi mana ya wane kalleni a wulak'ance, ya karbi kofin da tea aciki ya fasamun akai ya fashe akaina, sai jini nafashe da kuka ko kallona baiyiba, ina mik'ewa tsaye santsin tys din ya hade da tean da ya zube nafadi acikin glass dinda ya mutu tuni ya shige min jiki na gara ihu ba mai taimako sai Allah..... By HAYATU BABA ZUBAIRU (admin Hayat hausa novels Hausa novels and fashion And Cool novel, makeup and cooking) WHATSAPP NO: 07039625239 🍃ETRAT🍃 25&26 Haka na mik'e da gyar naje toilet na wanke jikina, inata kuka, naso in kira sister khadee ingayamata halinda nasamu kaina ko akwai shawarar da zata bani, sai kuma na fasa sai naga wannan sirrinane nida shu'umin mijina, haka na hakura ban gayawa kowaba, kwanana uku in jinya, wanda ko falo bana fitowa, tea kawai nakesha bantaba shiga tashin hankali irin na yan kwanakinnan ba, duk jikina ciwo yake, ni duk abinda zaimun ya daina dukana kawai... ina zaune a falo lokachin na chika wata biyar chur a gidansa, amma ba wani kulawa, nida babu duk daya, na zaune afalona wanda kana gani kasan ina gidan hutu da niima, amma zuciyana chike take da bakin chiki da takaici, akai akai nakanje gidanmu da gidansu , na gaida iyayenmu, kuma su Abba suna sakashi yaje gidanmu kuma yana zuwa sosai.. wannan zuwan kuwa da iffat akazo bansan miyasaba yakeson Iffat ba, har yana wasa da ita, ina chikin wannan dogon tunanin na tarihina sai kawai naji "ana Auntie'..!!" nayi firgit nadawo hayyacina na je da gudu na rungumeta ina jin dadi ina dariya, shi kuwa ogan dama yanzu nima na waye nasan dawa nake rayuwa, banda harara ba abinda ke hadani dashi, naja k'anwata muka shige chiki naji dad'in zuwan Iffat ko banza itace abokiyar fadana agida, yar shekara takwas sai wayon tsiya. Ranar nayiwa iffat wanka, nima na shiga inyo wankan, kamin in fito na tarar ta bata duk jikinta da kwalliyan hauka, saman ido bakinta ko ina ta bata tana ganina tasan dukanta zanyi, tayi waje da gudu ni kuwa dama nasaba binta da gudu ko gida gata idan tana gudu baka iya kamota, sai dai in fadi, amma bana daina binta. Haka ma yau tafita aguje na bita tana fita tayi karo da Ameer ta wani dadumeshi "wayyo yaya Auntie zata dakeni...!!" tashige chikin rigarsa, ni kuwa wai saina kamota naje da k'arfina, hannu daya yasaka ya rik'enmin hannuwa biyu, yacewa iffat ta gudu dakinsa yana murmushi, dama daga wanka nake dagini sai towel, ai kuwa tuni towel ya zame yafadi k'asa, dagani sai pant, kawai gani haka agabanshi, sai naga ya sakeni ya tsuramin ido kunya tahanani duk'awa indauki towel dina, na duk'ar da kaina gasa ina jiran ya tafi in dauki, abina amma shiru kakeji, nidai bansan miyakeyiba, hasalima ni tsanarsa nayi, mun kai minti biyu a haka, sai naji dariyar Iffat tana kiran yaya kazo na boye, sai kawai naga ya duk'a ya dauko towel dina da sauri yana daura min, abin ya dauremin kai matuk'a, amma duk da haka ban daga kai na kalleshiba dan kunya da takaici. Sai da na tabbatar da yabar gun sannan nashige d'aki da gudu iya kunya, yau naji kunya da takaichi, wannan ja'irar yarinyar ta janyo min. Ina zaune bakin gado sai ga Iffat da Ameer sunzo, sau d'aya na hada ido dashi na kawar dan kunya, kuma nakasa karanto abinda ke cikin idonsa.. yace " Auntie kiyi hak'uri bazamu sakeba" nakasa yimasa magana, nay shiru da bakina yak'ara maimaitawa " Auntie kiyi hak'uri kinga har wanka munsake ko iffat?? " Iffat tacee " eeh kuma ba zan sakeba" haka yak'are surutunsa shida iffatu, bance musu komaiba yazauna ya shafamata mai, yasaka mata tufafi suka fita abinsu ,basu dawoba sai bayan sallar esha, dama duk dare suna fita, suje yawo ni kuma ina gida ina gadi, sun dawo abin mamaki yau harda ni aka yiwa siyyah, wai ta lefin da Iffat tayi ne, nidai banchiba, gari yawaye ta chinye abinta. Haka dai Iffat tay sati biyu agidana, Har ta koma gida, amma tun daga narar da towel d'ina ya fadi gabam Ameer, ban k'ara bari muka hada ido dashiba, shiko sai wani son yimin magana yake, ko miye dalili ohooo..! Yana dakinshi yarasa mi yake mishi yawo akai, wai miye mace?? miyasa da yaga halittar jikin wannan yarinyar yaji shok ajikinsa??? miyasa yakeson sake ganinta ayanda yaganta?? Tambayoyinda suke masa yawo a kai kenan, lokaci daya yasamu amsa adayan bangaren zuciyarsa, mace dai wata halittace mara daraja, kuma baiwa, kamar yanda ka dauketa ada, kanason ganinta ne kawai dan tak'ara bata maka rai, kawai k'ara nisantarta, tambaya ta uku kuma sai yay shiru, sabida bakadamu da mace ba, shiyasa kake son kaganta ayanda kaganta.. Wannan lokaci dole in dauki mataki akanki karki kawo min chikas a rayuwa [5/16, 4:45 PM] Auntie M. Jabonation✍🏾: 🍃ETRAT🍃 27&28 Na Hauwa M. Jabo. Ya rasa mi yake masa dad'i, Tuni ya fita falo ya zauna gashi baya magana sabida mishkilanchi irin nasa, Bansan cewa yana gidan ba na fito da kayan bacci, gashi zuciya ta gama zugashi, yawani dalla min harara keee!! dama ke yake kirana, sabida ina kyautata zaton baisan sunana ba, na waigo mukai ido hudu sai ya kawar dakansa, ya mik'e tsaye ya finchiko mun gashina da qarfin balaee wandaa da kyar nake iya, nunfashi.. yacemun "Nanfa gidan musulmaine sabida haka kar in qara ganinki da wayannan kayan na arna, kinji abinda nafada" kinji fa fadan rashin dalili irin nasu Ameer, Yaci gaba, "oda yake mata haka kuke kamar dabbobi," ya turani da k'arfi na fadi tsakiyar d'aki, inda bakina ya daki tys din falon, goshina ma haka nanda nan bakina ya kumbura shafatain dina sukayi manya manya, goshi kuwa tuni yay wani jaaaa ina kuka ina dana sanin aurensa, wata kusan shida kullum azabar yau daban ta gobe daban, to wllhy nagaji nan nay tunanin gayawa sists khadee, sai kuma na fasa na tuna wannan sirrinane nace ko inkai kararsa gidansu? nan ma naga ba sauk'i, haka daai nay ta sak'a da war warewa.. To shi wannan mutumni so yake kullum in saka hijabi hala??? Nandai ba maza suke shigowaba balle inche kishi yake, nasan wannan bazai taba kishinaba sabida sam ba k'aunata yakeyiba. nay kuka idona sukai hulu hulu ga baki ya kunbura ga goshi ya fashe nayi ta kuka har na godewa Allah. Naci gaba da addu'a sai yanzu nakejin cewa Wllhy da Mahbuub na aura bazan taba irin wannan wulaqantaba. Ankawoni gidan mutum mishkili wanda baisan darajar dan adam ba.. Tabbas Ameer baya cikin mazaje na gari, haka naji na tsaneshi muguwar tsana, kuma ashirye nake da yabani takardar saki na in k'ara gaba, sabida na tsaneshi amma kuma ya za'ay ya sakeni shine maganar??? Ba amsa haka dai na hukura bayan kwana biyar na warke sumul kamar baniba, sai dai ko kodan bana fitowa daga dakina, namaida tea da Indomie abinchina anan daki nake girkawa ina chinyewa, bana fita wajee bare in chi karo da mugun mutum mai bak'ar ziciya, ina kwanche adaki naji alamar tafiya, daga kan da zanyi sai naganshi fuska babu rahma, tun bai k'araso gunaba na fashe da kuka, ya finciko hannuna iya k'arfinsa, yace "baki da maraba da baiwa, so dole kina yimin girki inachi..." Tofa kinji wata sabuwa... nikuwa yanda natsaneshi ko zai mutu wllhy bazan masa girkiba... "kina jina??" nadaure fuska na share hawayena nace masa, "wllhy ko zaka kasheni bazan maka girki kachiba..! sai dai yunwa ta kasheka" ya kawo min naushi a baki, sai kuma yayi sa'a ya sameni, ya fasa min baki, haka ya wurgani akan mirror, tuni ya fashe duk kayan kwalliyar sukayo kaina, nan danan nayi sabbabin raunuka, wanda dole sai naje asibiti inata kuka nafito falo kenan sai nay karo da Umma mahai fiyar Ameer ETRAT!!! Miya sameki??? Nafada jikinta ina kuka wllhy umma.......... [5/16, 5:00 PM] Auntie M. Jabonation✍🏾: 🍃ETRAT🍃 29&30 Na Hauwa M. Jabo "Wllhy Umma na fito wanka sai kawai jiri ya kwasheni, sai na fada kan madubi ," "amma ai da ban mamaki yarnan, ya kikayi kika fada ajikin madubi kamar an wurgaki, kalli bakinka fa" gabana yafadi RAS..!! araina nace mugun dankune kuwa ya wurgani.. nay take nace "Aaah Umma faduwa nayi" muka isa asibiti nanfa aka sakamin bndg ajiki ta ko ina da naji ciwo, bamu wuce gidaba gidansu muka wuce, anan umma ta fahinchi akwai wani abu tsakaninmu, amma kuma ni nak'i fad'in ko daya, aka gaji aka barni, na warke sumul amma banason komawa gidan azaba.. Haka yazo ya daukeni na koma kurkukuna, narame nay bak'i bakomai sai ido narasa miyake mun dadi ranar haka kawai naji natsani kaina kamar in kashe kaina, ga wani ciwon kai da yake damuna, atak'aice dai banjin dadin jikina, haka nay wanka nasaka wani riga da wando wanda yay balaeen fitar da surar jikina, naje kitchen ina hada abinchi sabida nagaji da chin indomiee, kuma yanzu ashirye nake idan yatabani zan tabashi, ina aiki dai ba lafiya haka na tsaya ahankali ina aiki amma banajin dadin jikina ashe mugun mutumin yazo yazauna yana kallona ta baya, yau yakasa danna iPad d'insa, sai tambayoyinsa suke masa yawo akai yana k'aryata amsar da dayan bangaren zuciyarshi ke bashi, sai yanzu ya tuna da wani abokinsa ya ce masa Ameer duk lokacinda kafara son wata mace zaka gane cewa mace ba baiwa bace baiwa ce... kuma ni'imace... mace tanada wasu ni'imomi masu yawan gaske wanda Allah yay musu acikin jikinsu, Allah yace su halittace mai sanya natsuwa tsakanin mu, dayawa abokinshi yakan gaya mishi siffofin mata masu niima, wayanda duk yagansu a jikin wannan yarinyar ya elaheee...!!! Yama sunanta!? dayan zuciyarsa ta tambayeshi babu amsa Lallai bai san sunanta ba ikon Allah... Miyasa nazauna ina kallonta!? dayan zuciyarsa tace sabida matarkace. Matana...!!!? To mizan mata!? insota kenan!? sai dayan zuciyar tace masa ai dan kana sontane kadamu da ita JALLAL KHALEQ....!! Anya nine kuwa!? sosai kaine AMEER HUSSEIN!!! A'ah abin da yakasa ganewa shine miyasa yakejin k'irjinsa na dukan uku uku idan bai gantaba!??? Miyasa yake damuwa da alamuranta!??? Miyasa yake son k'ara ganinta a yanda yaganta ranar da towel dinta yafadi!?? Kai tambayoyi sun mishi yawa miyasa.......?????? K'arrar faduwar abu yaji tarrrr.. da kuma tar watsewar plate yana zuwa sai ya ganta kwance kaman ta mutu inna lillahi wa inna ilaihi rajiuun...!!!! [5/16, 9:46 PM] Auntie M. Jabonation✍🏾: [5/16, 6:40 PM] Auntie M. Jabonation✍🏾: 🍃ETRAT🍃 31&32 Na Hauwa M. Jabo Yana k'arasa wa, Anan yaganta sumammayi, rana ta farko da mace ta bashi tausayi, yarasa mizai mata, kawai ya dagata chak yakaita mota, suka nufi asibiti aka bata gado, nan likita yace masa damuwane yay mata yawa, da kuma k'aranchin jini da yake damunta, anan fa yace azo adibi jininsa asaka mata. Ikon Allah wai Ameer ne zai bada jininsa ga MACE?? Abin mamaki kuma abin alajabi, wanda shi kansa baisai dalililn da yasa yake yin abinda yake shirin yiba, Dr yazo Ameer ya bada jininsa aka auna da nata, duk O+ ne, yayi dai dai da natan, haka kuwa yakwanta aka dibi leda biyu aka dura mata, aka saka mata ruwa leda daya, sannan ta farfad'o aka samu ta dawo hayyacinta, tana bud'e ido tayi salati, sai ta fashe da kuka Dr yazo yan tambayar lafiya?? "Ni ku sallameni wllhy gida nakeso" nan Dr yace tabari mijinta yazo yay signing za'a asallameta, tace itakam batada miji ita kadai take, akace yayanta to, namma tace aa sai ga Ameer yashigo yana zuwa naga ya daure fuska yacewa Dr. lafiya??waishi kishi tofa!! nima jabo da nake kawo muku rahoto abin ya bani dariya wai Ameer Hussein ne yake KISHIN MACEE... Dr. yace "No ba wani abu bane sir, tace a sallametane, nace ta bari mijinta yazo wai batada miji" Ameer yacewa Dr "Ok kaje ina zuwa" yana zuwa ya wani doro min hannu akan goshina, yace "bakida zazzabi sannu!" Ya sauke hannun sa, haka naji hannunsa kamar ya d'aura min wani garwashin wuta, dan zafi nagara jin tsanarsa araina, sai likita ya lek'o yace "Ameer Hussein baka gayamana sunan matar takaba, zamu cika form ne" nanfa kunyar duniya ta isheshi ya wani juyo ya kalleni, na banka masa harara, wanda yasa ya saukar da kansa k'asa, yabi likitan bansan yanda suka yiba ya dawo, yace in tashi mutafi nanfa nace ni gidan ubana zanje, kuma bazan shiga motarshiba, nan ma wani sabon rikici haka dai naga kamar yawace aganmu a asibiti muna saida hali nan dai na daure na shiga motarsa na zauna baya yanayi yana kallona ni kuwa banda harara ba abinda ke hadani dashi. Muka isa gida nasauka mota na shige dakina na kulle. Yakawo min magani anan yaji k'ofa gam, yau ake yinta, sai yanzu tambayoyinsa da yasaba yi suka rik'a dawo masa, tuni ya kawar da tambayoyin yaje yadauko key ya bude k'ofar, yata ya shigo tawani dalla masa harara, ikon allah koni jabo abin ya bani mamaki kunsan mi nagani?? HAWAYE a fuskar Ameer Hussein, wanda saida na girgiza hmmm aranta tace munafuki kuka kakeyi sabida ban mutuba ko, Ameer Hussein ya matso daf da ita ya riqe hannunta taso ta k'wace, amma takaasa haka tabar mishi hannuwa ya fashe da kuka kamar jaririn yaro yace mata.... 🍃ETRAT 🍃 33&34 "Dan Allah.....!!!" sai kuma yay shiru nanma yachi gaba da kukanshi mai tsima zuciya, amma kuma koda gwayan zarra ban tausayawa kukanshiba, hasali ma wani sabon tsananshi ne ke dada mamaye zuciyana. Ahankali naji kukan nashi ba mai k'arewa bane na sabule hannuwana nakoma falo, yayi kukansa mai isarshi, sannan ya tashi ya tafi d'akinsa, ai kuwa yaje daki tambayoyishi suka kara zo mishi kamar dai yanda yasaba duk tmbayar ta tazo sai ya bata amsa negative mai makon da da duk positive ne, ya natsu sosai yanason yagane miyasa yakejin abinda yakeji, Lallai son yarinyarnan ya kamani, tashin hankali..!! dama haka so yake? kodai sha'awace? sabida abokinsa yagayamasa akwai so akwai kuma sha'awa, tabbas son yarinyar nan nakeyi, ya akayi haka? ohoo.. Mi yasa to yake sonta??? Tabbas sonta yakeyi ai kuwa zaisha wahala sabida ya riga ya b'ata aikinsa, sai yanzu ya tuna wata shida chur da aurensu dai dai da rana daya baitaba kyautata mataba, toma wai miyasa nadamu da yarinnyar nan? tabbas SONTA nake kamar yanda daya bangare na zuciyar sa yabashi amsa cikin gaggawa, tabbas duk wasu alamu da abokinsa yake gayamasa naso da kauna yana jinsu ajikinsa, shidai har yanzu yakasa gasgaska abinda yakeji.. Duk yanda yay da zuciyanshi na k'iyayyar mace ta dawo masa yakasa, saima wani tausayi had'i da nadama akan abinda ya aikata yakeyi, haka yayta tunaninsa har garin Allah ya waye bai samu yay bacciba ko kadan.. Nii kuwa tunda nabaro mishi d'aki nadawo falo tsanarsa ce takemun yawo azuciyana, haka kawai naji inason ganin Mahbuub masoyina na gaskiya. dayan zuciyana yacemun ki daina tunanin wani namiji, har yanzu fa matarsa kike, tuni nashare zancen Mahbuub araina nantake bacci yay awon gaba da ni, da mafarkai kala- kala dama ba sallah nakeyiba sai nay baccina tazarce har safee. Fitowan da zay yaje dakinta sai yaganta falo kwance tana bacci, zuciyansa ta raya mishi yaje gurinta haka kuwa yaje gunta tana ta bacci abinta yatsaya yana kallonta, aransa yace Lallai matanma suna suka tara, towai ma miyasa natsani mace??? Alhalin duk wani jin dadi da hutu yana tare da ita, nan take yaji yanason taba pink d'in labbanta ko a hankali ta d'an juya, haka ya baiwa rigarta damar dagewa kadan, wanda yasa saman k'irjinta ya bayyana lokaci daya yaji kwata kwata ya chanja yashiga wani hali wanda tunda mahaifiyarsa ta haifeshi bai taba jin irinsa sai kawai........ [5/16, 6:57 PM] Auntie M. Jabonation✍🏾: 🍃ETRAT🍃35&36 Na Hauwa M. Jabo Yaji bari yay hugn d'inta, nanma yakasa, yariga ya rude yarasa tantance miyakeji ajikinsa wanda ga dukkan alamu sha'awace ta motsa, nan dai yakai hannunsa ya rik'e hannunta amamakin sa sai kawai yaji tarik'e hannunsa gam, har tana murmushi wanda ya bashi damar kai dayan hannunsa yana zagayawaa akan labbanta nan ma ga mamakinsa yaga tai murmushi, shima yai murmushi aransa yace ta hak'ura tayafemin kenan.. Kai gaskiya yarinyar nan tanada kirki, dama mata haka suke da rahama.? baisan kuwa ita mafarki takeyiba, wai ta auri Mahbuub suna soyayyah...!! lokaci daya na bud'e idonna cike da jindadi sai kawai naga mutum agabanna ya rik'e mini hannu, wani sabon tsanarshi naji ya kamani, na kwace hannuna, na tashi zaune, na dalla masa harara, ya duk'ar da kansa sabida kunya, Lallai dole yaji kunya idan yasanta, sabida ya musgunamata, bance dashi komaiba nabi ta gefensa na wuce, naje nayi brush nayi wanka tafito tas, ga mamakina sai naji k'amshin abinchi, koda na fito sai naga Ameer yana hada break fast sai k'amshi ke tashi, abin ya dauremin kai azatona, ko ruwan zafi baisan yanda ake dafawaba, amma gashi sai k'amshi ke tashi, naso inshiga kitchen in hada nawa brk fast d'in, sai kuma naji bazan iya jerawa dashi guri dayaba, kawai bari idan yafito sai inshiga in had'a, ina zaune ina kallo na yana fitowa nikuma natashi nashiga kitchen sai yacemin "kee...." sabida har yanzu baisan sunanaba "kefanahadawa break fast..! sabida Dr yace kina hutawa," ko kallonsa ban yiba haka nashiga kitchen nafara hada abin karyawana yana tsaye yana kallona har nak'are nazauna inachi yana kallona duk sai naji wani iri, naso intashi sai kawai naji bari inshare karma yaga nadamu dashi, har na chinye naje kitchen nay wanke wanke nadawo nachi gaba da kallona, shi kuwa yananan zaune sai bina yake da ido, duk inda nayi yana biye dani da ido, ranar ko ruwa banga yashaba, haka ya yini yadan bani tausayi kadan ammafa tsanarsa tana nan cikin raina, wajen qarfe goma naga gabaki daya kalanshi yachanza ya rame yayi wani zuru zuru dashi, yabani tausayi sai nay dabara nazo da kayan tea na ijeye akan table dinda yake gabanshi wai ina nufin yasha amma ni bazan cemasa yashaba, kawai ni nahada nawane nasha ko motsi baiyiba yabani tausayi sosai dan kuwa har yarame ko azumi mutum yay yana buda baki, amma gashi har shadayan dare yayi baichi komaiba, nakasa cemaca yatashi yasha haka natashi nashiga daki nay kwanciyata, har bacci yay awon gaba dani dasafee anan natarar dashi kwance yana bacci nadubeshi yay balaeen bani tausayi sabida nasan baichi komaiba, but ya zanyi in bashi abinchi sabida ko bakomai musulumi ne dan uwana.... (Hmmmmm... wallahi mata akwaimu da tausayi) sabida lokaci daya zuciyata ta karaya bawai dan Ina sonsa ba, aah kawai dai nasan baichi abinchi ba, anan nafara tunanin yazanyi nace yachi abinchi, shiru kusan minti biyar sai natafi kitchen na fara hada masa break fast wanda zai rik'e masa chiki sosai, nan danan na hada abinchi kala kala nazo na ajiye narasa yanda zanyi intayar dashi sai na daure naje ta duk'a kenan na dago hannu zata tabashi sai ya tashi mukayi ido biyu ... [5/16, 10:44 PM] Auntie M. Jabonation✍🏾: 🍃ETRAT🍃 37&38 Na Hauwa M. Jabo Ya bude ido kunya ta kamata lokachi daya tarasa yanda zatayi, sai Allah yakai idonta akan phone d'inta, sai tawayance ta'dauki wayanta ta k'ara gaba, shi kuwa ya d'auka dama wayan zata d'auka, yatashi tsaye sai jikinsa yafara bari bashiri yadawo yazauna, yunwa yakeji sosai ga kuma abinchi agabanshi yatashi dagyar yana dafa garu, yaje yay brush yadawo, sabida shi ko ganintan da yakeyi yanasa ya k'oshi yazo ya zauna yasan abinchi banashibane, saboda tace ko zai mutu bazatay masa girkiba, haka yazauna abin duniya duk yabi ya dameshi sai saqe saqe yakeyi. Tana chin abinchinta sai sukay ido hudu yay balaeen bata tausayee sai tace masa "bisimillah" ba musu ba kunya yazo yafarachi, har suka k'are, yay godiya ko kallonsa batayiba, dama tausayani irin nata. Tun daga ranar dai tana girki dashi, sai dai yana shan wulak'anchi da kallon banza da harara, kai duk abinda zai fusatashi tanayi amma shi ko ajikinsa. Kumma haka yana chin abinchinta kullum.. Aka samu sati d'aya, taga kamar neman shiri yakeyi, ita kuma hanyar rabuwa dashi take nema, sai ta dauki matakin daina zama falo aikuwa haka yafi komi azaba agurinsa, sabida zai iya hak'urin rashin abinchi, amma bazai iya hak'urin da rashin ganintaba, ya sameta ya ya gaya mata bazai iya haqurin rashin ganintaba ta gaya masa magana mai zafi saida yayi jaaa dan kishin da yaji lokacinda tay maganar Mahbuub... Tun daga ranar bata fitowa saidai ta dugyre masa abinci ta wuce abunta, yanda ta ijiye abinchi haka take tarar dashi baichiba, sai kuma abun yana damunta, kwana biyu da fara boyewarta, ranar sai ta fito falo dan tun safee bataji mostinsaba, koda tazo taganshi akwance kaman yay bacci, har lokacin sallah azzahar yay bai tashiba, bata kuma tayar dashiba, lokacin la'asar ma shiru kakeji, abin yabata mamaki sabida tasan yana balaeen kula da sallah, da duk wani abu da yashafi addininsa. Akayi Magreeb shima shiru ba sallah ba zancen chin abinchi, tarasa yanda zatayi tatayar dashi abinda ya daure mata kai shine, kwanciya ko motsi bayyiba ballantana ya juya, sai kawai tayanke hukunchin tayar dashi yay sallah tazo takira sunansa ahankali, taji shiru, tak'ara kiransa haka ma shiru, sai ta dan bubbugashi nan ma shiru nan da nan sai taji matsananchin tsoro ta bubbugashi da sauri ina fa baya mosti nan danan ta girgizashi iya qarfinta amma shiru ta kwantsa ihu ba wanda zai jita agidan datake kuma bata iya daukarsa tuni tafita aguje bako takalmi ta kira mai gadi sukazo sukaga baya motsi, haka akaishi asibiti tay balaeen rudewa haka suka isa asibiti aka bashi gado likita ya dubashi iya dubawansa amma lallai bashida rai.... tuni tasanar da iyayensu duk sun hallara lokaci daya tafita hayyachinta dayan bangaren zuciyarta yace mata idan ya mutu sai ki auri Mahbuub masoyinki kinga kun rabu lafiya.. dak'arfi tace "NOOOOOOOOO.......!!!" Wanda duk akayo kanta, lafiya? tak'ara fashewa da kuka, sabida tasan duk abinda yasameshi itace sabida ya taba gayamata cewa..... "Duk abinda zaki mini ko horo da yunya, harara, idan ma zaki iya kadakeni zan iya jurewa amma bazan iya jure rashin ganinkiba, sabida ganinki yafiye mini chin abinchi, kece abinchin ruhina, kuma wllhy gaskiya nake gaya miki, bazan iya chin abinchiba matsawar bansakaki a idonava, kinfi komai muhimmanchi agurina," a lokacin na dalla mishi harara da kuma tsaki nace mishi "Sai dai kamutu kuwa bazaka ganniba idan ka mutu sai na auri masoyina Mahbuub......." tak'ara fasheawa da kuka tabbas nice, sabida yagayamin amma bankiyayeba kamar mahaukaciya tafara surutai tana nina jawo..! wllhy nice..! ku yafeeni wllhy nice..!! Duk abinda ya sameshi nice. Sunrasa gane mi take nufi tabbas tashiga rudani sabida yanzu ta tuna kwananshi uku baici abinchiba tabbas ita tace sillar duk abinda ya sameshi dai dai nan Dr yafito yace musu sai dai kuyi haquri Allah yayi masa cikawa haka kikaji ta lau tafadi nan koda rai ko mutuwa........ [5/17, 7:00 PM] Auntie M. Jabonation✍🏾: 🍃ETRAT🍃 39&40 Na Hauwa M. Jabo Umma mahaifiyar Ameer, tayo kaina tana kuka tana, "Shikenan ya mutu..!! shikadai Allah yabani aduniya, kuma kin kasheshi," nanfa Umma ta ci gaba da rera wani matsanancin kuka, ta rud'e gaba d'aya. "Shikenan narasa dan'a, dama shikadai Allah ya rayamin, Ashe rabon ni zan kasheshi da kaina ne, nida nai masa aure kuma nasan bayason mace a rayuwarsa, yar nan har yasaka miki doka miyasa kika taka dokar.? kince kece? ya kikay kika kasheshe kitashi kiyi magana...!!" Amma nima lokacin na riga na suma, dak'yar aka janye Umma daga jikina wanda ga dukkan alamu ta samu tabuwar hankali, aka kaini d'aki dagyar na farfado daga dogon suman da nayi, ina bud'e ido nace "ina yaya As meer?" kowa sai kallona yake natashi zaune nafara ihu, sai an kaini gun yaya Ameer, nanfa akarasa yanda za'ay dani, aka yiwa Dr. magana akan ya nunamin gawar Ameer Hussein, yace sai nayi shiru, haka nai shiru, aka saka min wasu kaya nabi bayan Dr. naganshi kwance tunda nake bantaba ganin gawaba sai yau, gawar ma ta mijina, wanda nice sanadiyar mutuwar shi, na daure nay shiru dama Dr. yace mini idan nay kuka zan fita, tuni na natsu naje gunsa na tsaya Ina kallon sa, na bud'e fuskarsa da aka rufe da wani mayafi green, na kalleshi rana ta farko da naji sonsa ya shiga raina, amma ba amfani tunda na kasheshi..! na kama hannunsa ahankali na rik'e gam, amma abin mamaki ba sanyi ajikinsa, wanda a islamiyanmu ance mana gawa tanada sanyi idan ta dauki d'an lokaci, amma shi sai zafi naji ajikinsa, na kallesa Lallai nay asara koba komai zaman aure yafi zaman zawarchi, amma yazanyi tunda na riga na kasheshi, lokaci daya wasu zafafan hawaye suka saukomin da natuna da sista khadee yanda take soyayyah damijinta wanda nay alk'awarin duk lokacinda muka shirya sai namishi soyayyah wacce tafi wacce sista khadee takeyi da angonta, amma ina mijina ya zama gawa, wasu zafafan hawaye suka sauka a idona ahankali na janye mayafin da aka rufe masa jiki yanada singlet ikon Allah arayuwa inason miji mai gashin k'irji gashi nasamu amma nakasheshi..!! Ahankali na dora kaina akan k'irjinsa ina zubar da hawaye, amma ba sauti, na k'ara matse hannunsa iya k'arfina, nayi minti biyar ahaka sai naji kamar zuciyarsa tana bugawa kadan kadan nay balaeen tsorata da naji ya motsa hannunsa dana rik'e, dama gawa na motsi..?? Idan ma kasheni zaiyi to yakasheni in huta... sai naga likitochi sun shigo aguje ashe har sungani a dakinsu ceawa yana nunfashi tuni aka kada ni waje, amma kuma sai naji kukana ya tsaya kawai son ganinsa nakeyi. Umma dai tanachan ba lafiya anmata allurar barchi, nan dai na zauna ina tunaninsa lallai na cutar dakai Ameer, koda kai ka koyamin tsanarka, kai ka koyamin ki'yayyar ka. Dr. Ne yafito yace mungode Allah ranshi yadawo, dama dogon suma ne sai dai jikinsa yayi wk sosai, so sai ankula dashi anan nay hamdala, angayawa kowa Ameer ya dawo amma kuma baya iya magana sai dai motsi da kai da yakeyi. Bayan kwana d'aya aka bamu izinin zuwa ganinsa, munshiga mu biyar iyayensa da nawa iyayen da kuma ni muna zuwa duk yay ma kowa murmushi amma ni ko kallona baiyiba, nanda nan nasha jinin jikina, duk naji natsani kaina sai ya buda baki kaman zaiyi magana ina dago kai naga ya tsuramun idoo ko gyabtasu bayayi, har sai da na tsargu sai naji ance. ET...! ETR...!! ETRAT...!!! Tabbas Ameer ne ya kirani wanda bantabajin yakira sunanaba sai yau..... 🍃ETRAT🍃41&42 Nazo da sauri zan matso gunsa sai naga Umma tatareni, tace "bazaki zo kashemin d'aba tunda Allah yasa bai mutuba ak'ara gaba da mugayen halaye...!! Ki fita ki bace mun dagani" haka naji maganar kamar saukar aradu yadago hannu irin inje gunsa, amma umma ta hana naja na tsaya sai kuma kuka ya subuchemin haka na juya na fita bansan ina zan nufaba gidan ubana zanje? ko gidan mijina? Haka naita saka a raina tabbas nasan yanzu ina son Ameer sosai, wanda nima bansan yanda nakejin abun arainaba, sai su Hauwa Jabo da suka san dadin soyayyah da zafinta, haka dai na yanke shawarar tafiya gidan mijina idan ma yasakenine sai maje gidan mu, haka kuwa na wuce cike da bak'in ciki. Iyayena suna gun amma basu cemata komaiba, tunda basusan miyake faruwaba, saima hak'uri da suke bata. K'awata sista khadee tazo duba Ameer asibiti wanda bata tarar daniba, taje gida tanamun fada yazan bar mijina indawo gida nanuna mata cewa nazo daukar kayan mune nan dai nasamu narabu da uwar iyayi sista khadee.. hardai ameer yay kwana uku banje na dubashi ba Amma zuciyata tana Chan tare dasu. Acan kuwa ya matsa shi sai an kirani, Umma kuwa ta hana yace shiko sai an sallameshi. Haka aka salleshi yanata jin dad'i ga mamakinsa sai yaga an wuce dashi gidansu, ba gidansaba, yaso yay magana sai yay shiru suna isa gida su mama sukayi Allah yak'ara lafiya suka tafi gida, Umma kuwa nan tafara balaee wllhy sai ya sakeni, Ya tambayi dalilin hakan Umma tace sabida tanason takashe min kai... Yai murmushi nan yagayamata abinda yafaru tun farkon auren mu har zuwa yau, Umma tay shiru , lallai tayi saurin son yanke hukunchi batare da binchikeba, bayan annabi ya umurcemu da kada Ku rik'a yanke hukunci da gaggawa ba tare da bincike ba, tay danasanin abinda ta aykata sosai, wanda har kuka saida tayi, sabida giyar son kai data kwasheta, kuma Lallai Etrat tayi hak'urin zama da Ameer, wanda ba yarinyar da zata iyayin irinsa batare da ta fallasashiba, nan dai tai mishi fada sosai kuma tace sai tarabasu idan baiyi hankaliba, suka tafi dashi da ita chan gidansa, suka tarar dani a falo na zauna naci uban tagumi, daganina kasan ina cikin tashin hankali, naji tsoron ganin Umma, amma kuma naji dad'in ganin mijina wanda ya warke sai dai akwai rama kadan tare dashi nan muka gaisa da Umma a tsorace, itama tagane hakan, nan dai Umma tay ta bani hak'uri akan abinda tamun a asibiti, kuma tace " Ameer yafadamin duk chutarki da yayi Ai da ki da kin masa fiye dahaka Wllhy, Amma yanzu kina free, idan zaki zauna dashi to shikenan, idan kuma bakyaso wllhy zan saka ya sakeki sabida cutar tayi yawa idan kuma zaki iya zama dashi to zabi nakine." tabbb nan naga Ameer Hussein yana gumi tabbas inason mijina, amma ina tsoron halin maza nay shiru nan dai Umma takatse min tunani tace ke muke jira nace Umma gaskiya..... 🍃ETRAT🍃 43&44 Gaskiya..... sai kuma nace "Umma ba komai na hak'ura zan iya zama dashi" hawaye ne suke mini zuba a idona narasa mi yake damuna kawai inason hada ido da mijina amma nakasa haka dai Umma tay mishi fada agabana sosai kuma tasaka mishi sharudda masu yawa nima tay min nasiha sosai sannan tatashi ta tafi..... kikaji guri tsit kamar bama gurin kusan minti biyar chan dai naga shirun yay yawa nace masa "ya jiki?" Yace "da sauk'i" Koda na d'ago idona sai naga yana zubarda hawaye, hankalina yatashi sosai amma sai na dake "ETRAT....!!!" Wllhy saida naji tsigar jikina tatashi sabida yanda ya kira sunan, kuma dama ban taba jin ya fadi sunanaba sai asibiti, sai kuma yau. Mamakin inda yasan sunana nake, sai yace mun "kina mamakin inda nasan sunankine? a katin auren mu na duba anan naga sunanki" nan dai yana hawaye yana bani hak'uri akan abinda yamun nan da nan naji na hak'ura koba komai yanzu inason mijina... Amma nakasa magana, yau ga namiji yana mun kuka koda yasha mun kuka, naji dad'in haka, nakasa magana yasake kiran sunana,. Wallhy idan ya kira sunana daga kaina har zuwa k'afafuwana nakeji, na daga kai na kalleshi nace " ba komai komai ya wuce nima ka yafemin abubuwan da namaka" sai hawaye ikon Allah mata da miji kenan haka ya matso kusa dani ya kamoni ya rungumeni har inajin dukan girjinsa yana gogemin hawaye yana yana rarrashina kaman wata jinjira har nay shiru.... A bangaren Ameer kuwa wani yanayi yasamu kansa aciki wanda baisan ko miyeba, tunda bai taba rungume wata ya mace arayuwar sa ba, gaskiya mata abinso ne yana ta tunaninsa kala kala..... Tay garfin hali tace masa yaje yay wanka suchi abinchi, yayi wanka yafito tass dashi, suka hada ido sukay murmushi dukansu lokaci daya... sukachi abinchi suka zauna suna kallo, shikam ita yake kallo ita kuma satar kallonsa takeyi har 11 na dare hmmmm nidai jabo sai murna nake naga sun shirya nasan zaay bayanin..... Amma sai ameer ya bani mamaki yace ETRAT kije ki kwanta dare yayi ta tashi tayi dakinta shima yay dakinsa... Sun bani haushi sosai yau kwanansu 10 dai dai,da daidaita kansu, amma haryanzu ba wani labari dukansu sun saki jiki da junansu wanda har wasa naga suna yi amma ba dayan bayanin. Amma dukansu basa bacci dadare kowa tunanin daya yakeyi sai da safee suke fitowa falo suyi bacci tare da junansu... Watansu 7 chif da aure ba wani bayani, nikuma hauwa jabo na gaji ina ganin haka zan barsu in kammala amma sai k'awata Zainb khalifa tace inyi hak'uri nachi gaba da binsu har muga mizasu haifa..... 🍃ETRAT🍃 45$46 Ai kuwa haka nachi gaba da binsu kamar mayya, kullum suna manne da juna sunajin dumin junansu, amma basa yin wani abu bayan kwanciya akan jikin juna abun yana burgeni yanda suke kula da junansu, yauma kamar kullum munchi abinchi sai yadan fita wajee, yana fita nashiga wanka ina fitowa daga wanka sai gashi ya dawo, wai yafasa fita yadauka nay bacci shiyasa yashigo dakina, sabida sab maya shigowa dakina, haka nayi karo dashi sai naji kunya, amma sai na bayar ya kuwa budemin hannuwa irin inzo, ni kuma da sauri nafada ajikinsa yamaida hannuwansa ya refe ya rungumeni ya matseni sosai, wanda saida naji zafi a girjina, sabida baitaba rungumeni kamar yauba, sai nayi k'ak'arin raba jikina da nasa, amma sai yak'ra matseni a kunne ya radamin cewa "karkiji tsoro ETRAT NI K'AUNARKI NAKEYI, SONKI NAKEYI, WANDA AJININ JIKINA YAKE BAWAI SHA'AWARKI NAKEYIBA ..... Ki kwantar da hankalininki amma tabbas ina matuk'ar son ganin yaro ko yarinya wacce zaki haifamin." Bance masa komaiba, na k'ara lafewa, mun dade atsaye sai ya janye jikinsa yamun kiss yace inshirya yana jirana a falo, naso ya chi gaba damun waiwayin da yakemun, amma kuma sai yace inje in shirya, haka naje nasaka tufafina nazo mukayi labari yanda muka saba, har lokacin bacci yayi, mukayi sai da safee naje dakina, na cire kayan jikina wata rigar bacci na, nasan mijina yanason kusantana, kawai yana ganin kamar bana sone shiyasa yake dan kaucewa ,amma yau angama haka natashi na rasa miyake mun dad'i, ya zan bullowa al'amari tabbas inason in kwana da mijina, kodan na faranta mishi, amma bansan yanda zan yiba, ina zaune sai na tuna da indo matar dan sarki yanda ta jawo yarima gurinta, nace ko haka zanyi ? sai kuma nace aah bazanyiba, nan dai na yanke shawarar bari in hak'ura kawai inyi baccina har ranar da Allah zai sa ya kawo kansa, ina kwantawa sai naji an turo k'ofa, Ameer ne a tsaye yay mun murmushi sai yacemun yau naje nakwanta sai nariga jin tsoro, araina nace lallai ma namiji da tsoro, nay murmushi nace to zomu kwanta anan, yakuwa shigo araina nace gara ma da banjebaa gashi yazo da kansa, yamatso yatsaya yana kallona sai yanzu na tuna kayan da nasaka banga laifinsaba, nandanan sai naji kunya ya kwanta nima nazo na kwanta yace in matso muyi labari, da yake na sama kwanciya kusa dashi ban ji komai ba, nakuwa matso abina muna ta hira ta soyayyah, bansan yanda akay hannuna yakai saman k'irjinsa ba, nidai inason gashin k'irji a gun namiji, gashi na samu agun mijina, muna hira hannuna na kai kawo a gurin a hankali wanda sai naji dukan k'irjinsa ya chanza, yanzu yana bugawa sosai fat!.. fat!!!. sai na janye hannuna ahankali, yayi shiru nace "Saida safe" Nak'arara shigewa ajikinsa, sosai nanfa naji abu yasha banban dan kuwa gabaki daya Ameer ya rude, kawai naji yana neman wuce gona da iri, ni Jabo da ganin gwagwaf nafito da gudu ai kuwa ina dawowa zainb khalifa ta maidani wai sai nagano musu yanda aka k'are nanfa nakoma amma nayi latti sabida sun riga sun gama abinda zasuyi sai kukan Etrat nakeji, shikuwa Ameer yanata aikin rarrashi, nan dai na tabbatar da komai ya wakana, lallai Etrat taji jiki sosai, dan kuwa Ameer Hussein dai dai da rana daya bai taba kusantar wata maceca arayuwarshi, sai matarshi ta sunna nan dai yayi jinyar Etrat har ta warke kwana biyu nanfa yanemi amaimaita batak'i ba sabida tasan ba kew hana mai house abinshi, amma dai tana jin tsoro sosai, haka dai tabashi hadin kai har Etrat tasaba nan sun saki jiki da juna, tunda ya gane dawar garin kusan dai kullum ne, tun abin yana damun etrat har ya daina damunta, itama tadaina damuwa, soyayyah suke da k'aunar juna suna kula da junansu sosai.... "MATA akwai ni'ima ba halittar da takai mace daraja aduniya cewar Ameer Hussein......." Sista khade tazo gurina muna tadi wai taga na chanza k'irjina ya fito, nandai tace tana ganin nakamu, nikam banida wani ciki haka kuwa akayi nakamu wata uku bansaniba. Murna agun Ameer ba'a magana, lokachin haihuwa yayi na haifi yarona lafiyayye aka saka masa Aliyu ... Ranar yaya Ameer yadawo yaganni da hijabi "lafiya kike zama da hijabi kamar wata malama?" nace "kasan nan gidan musulmaine ba gidan arnaba." nanfa yatuna da dukan da yayimin na rashin dalili wai nazauna a gida ba tufafi kamar gidan arna, nan yaji kunya yayo kaina nagudu nafadi akan gado, "Ai baki saniba lokacin kin fara sauyamin tunaninane, shiyasa nace miki hakan" Haka suka chi gaba da rayuwar gwanin ban sha'awa, Sun shirya zuwa yawo, sukaje Cyprus daga nan sukaje Turkey gaskiya k'asar ta burgeni sosai sabida ba ruwan kowa da kowa daganan suka wuce mashhad, suka kawowa Hauwa jabo ziyara inda suka tarar da ita abin tausayi, sabida dai itama Ga dukkan alamu ta nuna tanason tayi Aure amma kuma karatu takeyi muna mata fatar alkhairi....... TAMMAT BI HAMDILLAHI. SAI KUNJINI A LITTAFI NA GABA MAI SUNA "AURE KO ZAMAN GIDA" DAGA TAKU HAUWA M. JABO....

Shin Ana Bukatan Blog ko website Kamar wannan kodai kamar Shafin Duniyan Fasaha, za'a iya samu a kan farashi mai rahusa daga Babban kanfanin Be With Me Technology Yola, Wayanda suka kware wajen Website Design da kuma hada Mahajar Waya. Za'a iya tuntubansu anan ko a wannan layin +2349039016969

Get Professional Website Design For your business Today Here. You can also visit our Tech Blog for more awesome Information. 
adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *