Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Friday, February 3, 2017

AN YI WALK'IYA COMPLETE

adsense here 💫💫AN YI WALK'IYA 1-3💫💫 ©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo ®NHW Da gudu take hawa kan matattakalar benen, kamar zata fad'i, tana k'wala kiran "Mummy! Mummy!!" da sauri Mumyn ta fito daga wani d'aki, tana cewa"lafiya?? Arfat irin wannan kira haka! sai ka ce wadda ta yi gamo?." A jiyar zuciya ta sauke, tare da k'ank'ame Mummy, sannan cikin shagwaba tace " Mummy ba yaya Abeed ba ne ya biyo ni, wai sai ya dakeni," "Duka! Ai ko ruwan sama bazai dakar min ke ba bare shi, wai ma to me kika masa da zai dake kin?" Arfat na shirin magana ya k'araso gurin yana fadin"Yauwa Mum mik'o min ita, Allah yarinyar nan yau sai na 6a66allata a gidannan, don akanki zan huce haushi ". Ya k'arashe maganar yana k'ok'arin janyota daga jikin Mum. Mummy tace"Nak'i na mik'o ta, kaji yaro, amma bakada ma kunya, ai ko mutuwa na kunyar idon mahaifi, yarinya har bayan mamanta ta b'uya kana a mik'ota, sai kace wata y'arka, wai kai me yake damunka ne Abeed? Mai ya faru kake neman 6a66alamin yarinya haka,?" Abeed yace "Mum yarinyar nan tana zubar min da class Wallahi,ke kuma kina wani kakkare mata," ya fad'a yana wani yarfee hannuwa, yana juya jikinsa irin dai yanda hadaddun guyz sukeyi d'innan "Mum wata nataciyyar yarinya ce ta lik'a min, ita kuma ta wani mak'alemun, kamar mayya haka take, Allah Mum tafi gum mannewa, kuma duk adalilin Arfat" ya fada yana nunata da yatsa yana hararanta, "don k'awarta ce, ita ta ba ta numberta, kuma ko Mum? Ba irin wulak'ancin da ban mata ba, amma ta k'i daina kirana dan naci irin nata" Mummy tace" haba Abeed ina laifin wanda yace yana sonka ? Yanzu dan Allah akan haka za ka dakar min yarinya, tanason ta had'a sunnar Annabi kai kuma kana shirme, to in gaya maka ban yarda ba." Arfat da ta la6e bayan Mum tace " Mum kuma ba ki ganta ba, Allah ta hadu na k'arshe bakiga yanda take yarfa gayuba" Danllah rufee ma mutane baki, ya ja dogon tsaki, "had'uwarta ta banza, ke wai yaushe zaki gane cewa yanzu komai saida Coins ake yinsa,? Yanzu gaya mun waye babanta a k'asar nan.? 'yar gidan malam Shehu da ita ta zo tana damuna kawai". Mummy murmushi kawai ta yi, dan tasan k'arshen zancen kenan yace talakace, " Talaka bawan Allah nidai M. jabo da M. Twins munsan cewa talauci daga Allah ne, haka dukiya ma daga Allah, mafi d'aukaka da soyuwa a gurin Allah shine maki tak'wa a cikin bayin Allah " Mum kam idan da sabo ta riga ta saba da halin Abeed, tun bai kai haka ba, halinsa ke nan tun yana yaro, tun tana ganin kamar k'uruciya ne, har yazo ya girma bai daina ba, yanzu kam har ta daina tunanin yarinta ne, don shekarunsa ya wuce a kira shi da k'aramin yaro.! "Dallah b'ace mun da gani, kamin na k'araso na makeka kamin ka maketa a gun," yayi gwafa, ya gangaro yana guna guni, "ke kuma idan na kamaki I will show u." ************ Alhaji Bashir Nasari, shine cikakken sunan mahaifinsu, haifaffen garin kano, kuma hamshak'in d'an kasuwa ne, yana da arzik'i sosai don yana d'aya daga cikin manyan 'yan kasuwa a jahar kano. Matarshi d'aya Hajiya Maryam, wadda suke kira Mummy. Allah ya azzurtashi da yaransa uku Muhammad da ake kira da Abeed, sai Arfat sai kuma Afrat. Gida ne wanda mamallakan sa suka gina cikin so da k'aunar juna, ga ilimi dai_dai gwargwado suna da tarbiyya. Sai dai Abeed ya fita daban, akwai girman kai da Jin shi wata tsiya ne, uwa uba rashin ganin talaka da gashi, don shi duk abinda zai had'ashi da talaka baya son shi kwata_kwata a rayuwarsa Don haka ya k'udiri niyyar shi ba zai yi aure ba sai 'yar wani babban mai kud'i a k'asar nan ko a duniya baki d'aya. Duk da iyayenshi suna nuna masa illar hakan amma ba abunda ya chanza daga halinsa..... Www.jabohauwa.WordPress. com Www.hauwajabo.blogspot.com M Twins 😍 Auntie M. jabo🍃 [4/11, 2:54 PM] 💫💫AN YI WALK'IYA 4&5💫💫 ©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo ®NWA Misalin 8:30AM, ya fito cikin shirinsa na zuwa office, saboda shine MD. na babban companyn Daddy dinsu, dake sharad'a phase 2. Direct dinning area ya nufa, da nufin yin breakfast, karaf idonsa akan ladi, ya hango ta (d'aya daga cikin masu aikinsu) ta gifta ta wurin dinning table d'in, hakan shi ya tilasta masa tsayawa tare da k'wala mata kira, jiki na rawa ta k'arasa inda yake tace"ga ni yalla6ai " " ke wai wani irin kunnen k'ashi ne da ke ? Eh? Sau nawa zan ce dake idan an kawo mun abinci kada ki kuma zuwa ko hanyar da aka bi aka wuce da abincin, bare kuma kusa da shi"? cikin rawar murya tace "don Allah ka yi hak'uri, akasi aka samu yallab'ai, naga har takwas da rabi na d'auka ka tafi ohis, shiyasa amma ba da niyyar zu....... " ya katseta tare da fad'in "shut up! tashi ki ba ni wuri 'yar sa'ido kawai, har an san lokacin da nake fita da kuma lokacin da nake dawowa, munafukai 'yan sa ido"jiki a sa6ule ta mik'e ta fice daga parlourn. Wani wawan tsaki yaja, sannan ya juya a yangace ya hau kiran Afrat , da d'an hanzarinta ta fito daga d'akinsu tace"ga ni yaya" Abeed yace "waye ya yi girkin can ?" tare da nuna mata da hannu, tace" haba sai ka tambayi wanda ya maka girki, ni na yi mana" ya harareta "ke banason rashin kunya kinaji, are you sure ke kikayi,?" Kamar ba zata amsaba chan ta ta gyad'a kai tare da cewa "Im pretty sure". Yace "kin dai san halina duk ranar da ku ka sake ku ka bawa 'yan aiki girkina sai kun gayawa aya zak'inta, tace" haba yaya ai ba ma ba su, ni ko Arfat muke yi, "gud kya iya tafiya", ta wuce aranta tace "sau nawa kana lamushe girkin yan aiki, har kana santi, wane mara aikin ne zai zaman tashi tunda asuba yana maka girki, sai kace wasu matanka," ta wuce d'akinsu, ya zauna ya yakuci wannan ya tsikari wanchan, duk jarabarshi baya iya chin abinci sosai, ya k'are ya wucee office... ****** Misalin k'arfe12 na rana Mubarak babban abokin Abeed ya kai masa ziyara a office d'in sa, bayan sun gaisa yake sanar da shi zancen dinner da za a yi na auren abokinsu Jabir. Sannan ya k'ara da cewa "please Abeed ka yi k'ok'arin attending, don nasan halinka yanzu za ka fara kawo mun k'abli cikin ba'adi" Sai da ya d'aga hannayensa ya watsar alamar ko oho,!, Sannan ya ce " alright yanzu gaya mun venue da time na ji idan zan iya zuwa gurin",murmushi Mubarak ya yi yace "za ma ka iya zuwa wurin, don ba 6oyayyen guri ba ne". Abeed yace"No my man, ba abin da nake nufi ba kenan , I mean gurin ya yi had'uwar da kamar irina zai je wurin ko kuwa"? Mubarak hannunsa ya d'auka ya d'ora kan goshinsa yace "oh! Abeed ka na ba ni mamaki wallahi, wai mai......." hannu Abeed ya d'aga masa alamar ya saurara haka. Sannan yace"just answer my question " Mubarak yace" ok, a golden Dragon ne". Almost 5 minutes bai ce komai ba, har Mubarak ya gaji da shirun yace"ya dai? ba ka ce komai ba ". Sannan Abeed ya yamutsa fuska, wanda ya k'ara bayyanar da kyansa, a fili, "gaskiya ba zan je ba ne cox wurin bai mun ba!". Mubarak ye zaro ido cike da mamaki, "yanzu Abeed golden Dragon ne bai maka ba?" Kai ya gyad'a alamar Eh.. Mubarak yayi murmushi, dan yasan Abeed saida rarrashi, ya cigaba da cewa "gaskiya my man idan ka yiwa Jabir haka ba zai ji dad'i ba" Abeed yace"ban yi don na 6ata ransa ba, zan masa waya ma na bashi hak'uri, bana son zuwa guri ne na tarar da tarkacen mutane marasa aji a gurin, wannan ne kawai badan wannan ba zanje mana" "amma ai ka san waye Jabir! kuma ka San waye mahaifinsa a garin nan, so bana tunanin za'ayi k'aranta a gurin, ka sa ni ma ko ka had'u da wata 'yar minister acan ya fad'a yana murmushi. Ya tsine fuska Abeed ya yi, yace" ' ya'yan ministers ai suna suka tana, kamar 'yar k' aramin minister mai zan yi da ita" shi dai Mubarak ido kawai ya zuba yana kallonsa domin al'amarin Abeed ya girmi tunaninsa, da k'yar ya samu ya lalla6ashi ya amince akan zai je. Muje zuwa muji mizai faru a gun....... Www.hauwajabo.blogspot.com Www.jabohauwa.WordPress.com M Twins😍 & Auntie M. Jabo 🍃 [4/11, 2:54 PM] Wacce Zamuyi Book: 💫💫AN YI WALK'IYA 4&5💫💫 ©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo ®NWA Misalin 8:30AM, ya fito cikin shirinsa na zuwa office, saboda shine MD. na babban companyn Daddy dinsu, dake sharad'a phase 2. Direct dinning area ya nufa, da nufin yin breakfast, karaf idonsa akan ladi, ya hango ta (d'aya daga cikin masu aikinsu) ta gifta ta wurin dinning table d'in, hakan shi ya tilasta masa tsayawa tare da k'wala mata kira, jiki na rawa ta k'arasa inda yake tace"ga ni yalla6ai " " ke wai wani irin kunnen k'ashi ne da ke ? Eh? Sau nawa zan ce dake idan an kawo mun abinci kada ki kuma zuwa ko hanyar da aka bi aka wuce da abincin, bare kuma kusa da shi"? cikin rawar murya tace "don Allah ka yi hak'uri, akasi aka samu yallab'ai, naga har takwas da rabi na d'auka ka tafi ohis, shiyasa amma ba da niyyar zu....... " ya katseta tare da fad'in "shut up! tashi ki ba ni wuri 'yar sa'ido kawai, har an san lokacin da nake fita da kuma lokacin da nake dawowa, munafukai 'yan sa ido"jiki a sa6ule ta mik'e ta fice daga parlourn. Wani wawan tsaki yaja, sannan ya juya a yangace ya hau kiran Afrat , da d'an hanzarinta ta fito daga d'akinsu tace"ga ni yaya" Abeed yace "waye ya yi girkin can ?" tare da nuna mata da hannu, tace" haba sai ka tambayi wanda ya maka girki, ni na yi mana" ya harareta "ke banason rashin kunya kinaji, are you sure ke kikayi,?" Kamar ba zata amsaba chan ta ta gyad'a kai tare da cewa "Im pretty sure". Yace "kin dai san halina duk ranar da ku ka sake ku ka bawa 'yan aiki girkina sai kun gayawa aya zak'inta, tace" haba yaya ai ba ma ba su, ni ko Arfat muke yi, "gud kya iya tafiya", ta wuce aranta tace "sau nawa kana lamushe girkin yan aiki, har kana santi, wane mara aikin ne zai zaman tashi tunda asuba yana maka girki, sai kace wasu matanka," ta wuce d'akinsu, ya zauna ya yakuci wannan ya tsikari wanchan, duk jarabarshi baya iya chin abinci sosai, ya k'are ya wucee office... ****** Misalin k'arfe12 na rana Mubarak babban abokin Abeed ya kai masa ziyara a office d'in sa, bayan sun gaisa yake sanar da shi zancen dinner da za a yi na auren abokinsu Jabir. Sannan ya k'ara da cewa "please Abeed ka yi k'ok'arin attending, don nasan halinka yanzu za ka fara kawo mun k'abli cikin ba'adi" Sai da ya d'aga hannayensa ya watsar alamar ko oho,!, Sannan ya ce " alright yanzu gaya mun venue da time na ji idan zan iya zuwa gurin",murmushi Mubarak ya yi yace "za ma ka iya zuwa wurin, don ba 6oyayyen guri ba ne". Abeed yace"No my man, ba abin da nake nufi ba kenan , I mean gurin ya yi had'uwar da kamar irina zai je wurin ko kuwa"? Mubarak hannunsa ya d'auka ya d'ora kan goshinsa yace "oh! Abeed ka na ba ni mamaki wallahi, wai mai......." hannu Abeed ya d'aga masa alamar ya saurara haka. Sannan yace"just answer my question " Mubarak yace" ok, a golden Dragon ne". Almost 5 minutes bai ce komai ba, har Mubarak ya gaji da shirun yace"ya dai? ba ka ce komai ba ". Sannan Abeed ya yamutsa fuska, wanda ya k'ara bayyanar da kyansa, a fili, "gaskiya ba zan je ba ne cox wurin bai mun ba!". Mubarak ye zaro ido cike da mamaki, "yanzu Abeed golden Dragon ne bai maka ba?" Kai ya gyad'a alamar Eh.. Mubarak yayi murmushi, dan yasan Abeed saida rarrashi, ya cigaba da cewa "gaskiya my man idan ka yiwa Jabir haka ba zai ji dad'i ba" Abeed yace"ban yi don na 6ata ransa ba, zan masa waya ma na bashi hak'uri, bana son zuwa guri ne na tarar da tarkacen mutane marasa aji a gurin, wannan ne kawai badan wannan ba zanje mana" "amma ai ka san waye Jabir! kuma ka San waye mahaifinsa a garin nan, so bana tunanin za'ayi k'aranta a gurin, ka sa ni ma ko ka had'u da wata 'yar minister acan ya fad'a yana murmushi. Ya tsine fuska Abeed ya yi, yace" ' ya'yan ministers ai suna suka tana, kamar 'yar k' aramin minister mai zan yi da ita" shi dai Mubarak ido kawai ya zuba yana kallonsa domin al'amarin Abeed ya girmi tunaninsa, da k'yar ya samu ya lalla6ashi ya amince akan zai je. Muje zuwa muji mizai faru a gun....... Www.hauwajabo.blogspot.com Www.jabohauwa.WordPress.com M Twins😍 & Auntie M. Jabo 🍃 [4/11, 2:54 PM] Wacce Zamuyi Book: 💫AN YI WALK'IYA 9💫 ©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo ®NWA Cikin 6acin rai Abeed ya koma gida, parking kawai ya yi ko kulle motar bai yi ba, ya wuce part d'in sa, ransa a dagule yake gaba d'aya, yana tunanin wai yaushe ne burinsa zai ciki, ya samu yarinyar da ta dace da shi, wacce ya ke mafarkin samu, domin shi kansa yanzu ya hak'ik'an ce da ya na buk'atar aure, amma matsalar duk 'yan matan da ke sonsa yanzu ya raina arzikin iyayensu, duk da cikin su babu wadda za a d'auka ace babanta matsiyaci ne, don dai shi ya d'auki k'atoton buri ya sakawa zuciyarsa, dole sai 'yar mai hannu da shuni, lokaci d'aya ya tuna da wacce akace tanasonsa, wai babanta yayi rik'on logal government, dai rainin wayo, wani dogon tsaki yaja, yadan juya kwanciyar sa, ya kalli a gogon d'akin yana lumshe ido. ********* Goggo wacce nake tunanin y'ar uwar Dadyn su Abeed ce, zaune take tareda Mumy suna hira, Abeed ne ya shigo ya gaishesu cikin sakin fuska sannan ya wuce d'akin sa, nan suka fara hirar yau da kullum, har Goggo ta gangaro akan abinda ya dad'e yana damun ta, "hajiya yaran yanzu sai a hankali, sam basa tunani basa naziri, yanzu za ku ga wasu yaran masu kud'i idan za su yi aure sai su rik'a hangen wadda mahaifin ta ya dame nasu ya shanye da naira, don zilama, maimakon su nemi dai_dai su, tunda Malam bahaushe ma ya ce "dai_dai ruwa dai_dai tsaki, kuma kowace k'warya da abokin burminta" sannan ma ina laifin su yi k'asa_k'asa su nemi 'yar talaka bawan Allah suma su samu su lasa, kinga ai an taimaki juna an rufawa juna asiri ta wannan hanyar, amma ba a yi saboda buri ya cikawa masu irin wannan halin zuciya, kowa sai dai-dai shi," Mumy tace "Wallhy zancen ki dutse Goggon yara, nima abin yana damuna, musamman idan naga halin yaronnan banajin dad'i sam, amma kinsan kosu talakawan akwai nasu sabida sai su k'wallafa dogon buri wa yaran su, su mayar da yayan nasu kamar jari, domin wasu sai ka ga sun zaune jiran mai d'an maik'o_maik'o har yarinya ta tsofe a gida, ba iyayenba ba ' ya'yan ba, kije gida ki rasa gane uwa da yaran gida, akwai wani gida da mukaje ta'aziya, a gidan naga mata 'yar kyakyawa, wacce nake tunanin zata haifi yara biyu ko uku, nake tambayar matar gidan, an mata amarya ne, dan tare na gansu, sai take cemin ai 'yar kice wance, wallhy saida na kai zaunedDan mamaki, na tuna yarinyar sa'ar Muhammad ce fa! Amma har yanzu tana gida," Goggo ta saka dariya, " kin bani dariya, wai an miki amarya ne" itama Mumy dariyar tayi suka ci gaba da hira" wannan zamanin kowa kwad'ayi ya yi masa yawa, bayan sun mata Allah ke yin komai, domin kowa an riga an rubuta k'addararsa tun kafin ya zo duniyannan, we just trace, sai ka ga budurwa ta zauna jiran Mr right har ta tsofe tun tana samun masu zuwa har lokacin ta ya wuce ya zamana bata samu, ta tashi a tutar babu, k'arshe sai ta auri wanda bataso, sabida da yawa masu wannan burin, wallhy basa auren mazan da zuciyar su takeso, saidai dan kud'i, su tashi ba wan ba k'ani, ta yi haihuwar guzuma 'ya kwance uwa kwance, ba mai d'an maik'o_maik'o ba mijin kwatakwata" nan ma saida suka dara, Goggo tace, " nifa kina magana kina saka engilishi, kuma kinsan ba ganewa nakeyiba," sukayi dariya gaba dayan su, Goggo tace, " Allah ya sa masu wannan halin su gano su bari dan ba alkhairi acikinsa" ameen Mumy ta amsa dashi, Na kalli M Twins nace "nifa al'amarin Abeed yana bani mamaki domin ya d'ebo da zafi, kace sai 'yar wane ko wane," M. Twins tace " ?kedai bari Aunty Jabo, Allah na d'auka irin wannan abin matane kawai keda wannan hali, ashe har maza ma sunayi, abin kunya, amma hausawa sun ce "kowa ya d'ebo da zafi bakinsa"..........." Www.hauwajabo.blogspot.com Www.jabohauwa.WordPress.com M Twins😍& Auntie M. Jabo ✍🏾🍃 [4/11, 2:54 PM] Wacce Zamuyi Book: 💫AN YI WALK'IYA 8💫 ©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo ®NWA K'arasawa ta yi in da Mufeeda ke tsaye kamar an dasata ta ce "mufy ya na ganki a tsaye, bayan ya tafi dama nasan ba lallai ya amince da buk'ata na ba". Cikin yak'e Mufeeda ta ce "kar ma ki yi wannan tunanin Fadeela, zai so ki da yardar Allah, yanzu ma don bai ganki ba ne na tabbatar idan ya yi ido hud'u dake ba abinda zai hana ya so ki". A jiyar zuciya Fadeela ta yi, sannan ta ce "ta yaya zan kuma had'uwa da shi bare har ya ganni?? Kar ki manta, ko sunansa ban sa ni ba, bare in da ya ke". Murmushi Mufeeda ta yi, ta ce " idan akan wannan ne ki kwantar da hankalinki kamar tsumma a randa, idan kullum kike son ganin Abeed za ki gan shi da yardar Allah." Cikin mamaki Fadeela ta ce "wow! nice name, sunansa kenan"? Mufeeda ta gyad'a kai alamar eh, Fadeela ta cigaba da fad'in "amma mufy ta yaya zan gan shi duk lokacin da na ke so ya gaya miki sunan unguwarsu ne, ko wurin aikinsa ?" Dariya Mufeeda ta yi sosai sannan ta ce" wannan kuma sai kin ba da wani abu sannan zan gaya miki, "6ata rai Fadeela ta yi cikin sigar wasa ta ce" dad'ina da ke kenan, yanzu za ki fara ja mun rai tunda kin ga ina son ji ". Tafiya Mufeeda ta fara tana cewa" shi kenan tunda ba kya son ji, da tuni kin mik'o wani abu, "gabanta Fadeela ta tara tare da cewa" haba friendy ko haka ki ka bar ni ai kin ja mun rai, don Allah ki gaya mun", ta k'arashe maganar kamar za ta yi kuka. Mufeeda ta ce "don't cry k'awata, he's my cousin", waro ido Fadeela ta yi tare da daka tsalle ta rungume Mufeeda tana cewa "don Allah da gaske kike yi mufy"? Mufeeda ta ce" yes da gaske ne ko gobe ki ke so zan kaiki gidansu ya Abeed, "Fadeela ta kuma k'ank'ameta tare da cewa amma na ji dad'i Allah ya sa hakan ya zama silar cikar burina." Mufeeda ta ce "ameen, sannan ta duba agogon wayarta ta ce" gaskiya Fadeela dare yayi fa, gashi lunching d'in an fara a makare bari na kira driver ya zo, sai ya fara kai ki gida, sannan sai mu wuce ". Fadeela ta ce" gaskiya kam don kar ayi mana fad'a kinsan hajiya idan ta fara," suka saka dariya. Www.hauwajabo.blogspot.com Www.jabohauwa.WordPress.com M Twins 😍 & Auntie M. Jabo ✍🏾🍃 [4/11💫AN YI WALK'IYA 6&7 💫 ©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo ®NWA Tun da safiyar ranar mubarak yake ma Abeed waya akan kada ya manta please, yamai SMS ba adadi, k'arshe ya yarda zai tafi, dan har ya shirya dojewa. Sai wurin k'arfe tara da minti ashirin da biyar Abeed da tawagarsa suka shiga hall d'in, cikin takun isa da k'asaita yake tafiya, ya rufe idonsa da wani shade bak'i kaitsaye gurin da aka tanada domin zaman su suka nufa. Wohoho! Ku zo ku ga 'yan mata yanda suka zuba masa na mujiya suna kallo, kai basu kad'ai ba har mazan dake gurin kallonsa suke yi tamkar sun ga wata sabuwar halitta, shi kuwa gogan naku ko kallo ba su ishe shi ba, tafiyarsa kawai yake cikin isa da izza har ya isa wurin zaman su. Tun shigowarsa wata yarinya mai amsa sunan Fadeela, muka ga duk ta rud'e ta rikice, sai wani dube_dube take kamar mai neman wani abu. Sai can kuma muka ga ta nufi wani side na musamman, domin an yi decorating gurin sosai fiye da inda take zaune, Da sauri ta k'arasa wurin har tana tuntu6e, tare da rik'o hannun wata budurwa wadda ba zata wuce sa'arta ba, sannnan ta ce "Mufy ta so don Allah ki gan shi shine wanda na ke yawan yi miki maganarsa" ido Mufeeda ta zuba mata na d'an lokaci sannnan ta ce" wai ki na nufin guy d'in da ba ki da aiki sai na maganarsa shine ya zo nan gurin,"? Fadeela ta ce "eh tare da langa6ar da kanta gefe," Mufeeda ta yi farr da ido,sannnan ta ce "gaskiya fady kin ban kunya, duk yanda kika h'adun nan, kuma kike gwara kan samari son ranki amma ki 6ige da baran soyayya akan saurayin da ko sunansa ba ki sa ni ba". Dafa kafad'arta Fadeela ta yi tare da cewa "friendy ba ki ga guy d'in ba ne that's why kike wannan maganar, kin san first class guy, full options to shi ne, ni tsoro ma nake kar ki gan shi ki kasa controlling kan ki ki je ki shigar da kan ki ba ni ba" ta k'arashe maganar tare da sakin dariya! Duka Mufeeda ta kai mata, ta goce sannnan ta ce "an gaya miki akwai wanda ya isa ya ture gwamnatin k'albina ne," Mufeeda ta cigaba da fad'in "ni dai zo ki nuna mun in da ya ke, ga ganshi, na cigaba da abinda na ke yi". Fadeela ta ce "na ga dai sun nufi wurin da aka tanada don manya_manya abokan ango" ta fad'a tana d'an kalle-kalle OK, "to ta yaya zan yi na gane shi??" Cewar Mufeeda, nari mu je na nuna miki shi ko daga nesa ne, d'an nesa da su Fadeela ta tsaya take nunawa Mufeeda shi, ba tare da ko na kusa da su sun gane abinda suke yi ba. Tun da Mufeeda ta hangoshi take wasiwasin wani abu a zuciyarta, sai da ta zo daf da shi sannan ta tabbatar da abinda take zato. Sallama ta yi sannan ta ce "sannu yaya Abeed" Jin an kira shi da yaya, ya tilasta masa d'agowa da kan sa domin ganin mai magana. Fuskarsa ya d'an saki sannan ya ce " yawwa sannunki", ta cigaba da fad'in ashe kai ma ka zo bikin k'awarmu"?? Jin bai ce komai, ta ce "angon ne abokinka ke nan"?? kai ya gyad'a mata kawai, ta ce" ai ni amaryar ce close friend d'ina". Jin ya kuma shiru ta ce "yaya ba ka son zuwa gidanmu su Arfat ne kawai ke zuwa". Hmm! kawai ya ce, nan ma shiru ne ya kuma ratsawa, sai da ta ga shirun yayi yawa ta ce "dama akwai maganar da ta kawoni wurinka idan ba za ka damu ba ka ba ni 5 minute's please", kamar ba zai yi magana ba, sai can ya mik'e ya yi mata nuni da su fita daga gurin. Gefe suka koma, sannan ta fara masa bayanin abinda ya kawota, ta k'arashe maganarta da cewa don Allah yaya ka taimakawa k'awata ba ka ga yadda ta ke sonka ba." Bud'ar bakinsa sai ya ce "waye mahaifinta"? Cikin rashin fahimtar maganarsa Mufeeda da ta ce" Babanta dai d'an siyasa ne", ya ce "muk'amin meye da shi"? eh, to ni dai abinda na sa ni ya ta6a rik'on k'warya a local government". "What!" ya fad'a da k'arfi, yana had'e fuska, daga haka bai k'ara cewa da ita komai ba, sai ga ni ta yi yana niyyar fita daga hall d'in ba ki d'aya. Da sauri ita ma ta bi bayansa,bayan ya isa in da ya ajiye motarsa yana k'ok'arin shiga, ta sha gabansa tana fad'in "haba yaya Abeed ba ka ce komai ba, ba ka ga yanda yarinyar take mutuwar sonka ba". Ai kuwa sai dai ta mutu in dai ni ne, I hate her, ya fad'a tare da shigewa mota ya ja da k'arfi da niyyar ficewa daga wurin, dai_dai lokacin Fadeela ta fito.......................... Www.hauwajabo.blogspot.com Www.jabohauwa.WordPress.com M Twins 😍 & Auntie M.Jabo ✍🏾🍃 [4/11, 2:54 PM] Wacce Zamuyi Book: 💫AN YI WALK'IYA 10&11 💫 ©Mrs Saif & Hauwa M Jabo ®NWA Bayan kwana uku Mufeeda da Fadeela suka yi shirin zuwa gidansu Abeed don gaishe da Mumy, sun taki sa a kuwa don sun tarar da Arfat da afrat suna gida, su na yin sallama, Arfat ta taso da sauri ta rungume Mufeeda tana fad'in "oyoyo! Mufeeda yau a gidanmu" ? Kafin ta yi magana, Mumy ta fito, nan da nan ita da Fadeela suka zube su na gaisheta, cikin fara'a Mummy ta amsa musu, sannan ta ce "Mufeeda shiru kwana biyu kin daina lek'o mu". Mufeeda ta ce "eh wallhy Mummy school ne ya 6oyeni", mummy ta ce " ayya!, nima nasan Mufeeda akwai zumunci, to Allah ya ba da sa a", suka ce ameen ". Sai kuma ta kalli Fadeela ta ce da Mufeeda" Wannan k'awarki ce "? Murmushi Mufeeda ta yi tana kallon Fadeela ta ce" eh, Mummy k'awa ta ce " Allah sarki ya sunanta"? Tace" Fadeela ", sannu Fadeela Mummy ta fad'a tare da mik'ewa ta na cewa" Arfat haka za ku bar bak'in naku ba d'an abun ta6awa "? Afrat ta ce" Mummy dama yanzu na ke son tashi", ya dai kamata Mummy ta fad'a tare da shigewa kitchen. Sun sha hira sosai, sannan daga bisani Mufeeda take ce da Arfat ya Abeed na nan kuwa?? Arfat ta ce "a'a, ina za ki ga ya Abeed yanzu, ai sai wurin k'arfe biyar yake dawowa daga office". Mufeeda ta ce "ok, Arfat ta ce" ko ta samu ne "ta fad'a tana murmushi, ita ma Mufeeda murmushin ta yi, sannan ta ce "sosai kuwa, Fadeela ce ke masifar son ya Abeed," Arfat ta ce "wow! ai kuwa ina ganin Fadeela na ji ta kwanta mun a rai, Allah ya sa ya Abeed ya amince, gaskiya da ya yi mata". Sai kuma ta mik'e da sauri ta na fad'in bari na je na sanarda Mummy ta zo ga sirikarta", Fadeela ta hanzarinta ta rik'o hannun Arfat tana Murmushi ta ce "don Allah kar ki gaya mata yanzu bari sai mun tafi Allah kunya nake ji, ita kanta Mufy ta san ba halina ba ne cewa ina son wani kawai na d'auki son yayanki a wani 6angare na k'addarata, amma kwata_kwata mace ta ce tana son namiji baya burgeni", ta k'arashe maganarta da d'an guntun hawaye. Dukan su jikinsu ya yi sanyi Arfat ta ce "in dai mummy ce ba ta da matsala Allah ki daina ma Jin kunya don ta saba ganin 'yan mata kala_kala masu zuwa neman ya Abeed". Har wurin k'arfe shida Abeed bai dawo ba, don haka suka yi shirin komawa gida, mummy ta had'a musu sha tara ta arziki, sannan ta saka driver ya kai su gida. Sai wurin k'arfe bakwai ya shigo gidan , bayan ya yi wanka ya ci abinci, mummy ta same shi tace ta na son yin magana da shi. Murmushin gefen kumatu ya yi sannan ya ce "ina Jin ki Mum". Mummy ta fara magana "Abeed dama akan maganar aurenka ne, gaskiya ya kamata ka nutsu kasan mai kake yi zuwa yanzu, ka ajiye duk wani shirme da ke ranka, ka za6i matar aure ka yi aurenka ya fiye maka, kuma mu ma zamu fi samun kwanciyar hankali, don na gaji da zaryar da 'yan mata ke mana a cikin gidan nan". Juyo da dubansa ya yi sosai gareta, sannan ya ce "Mum yau ma wata ta zo kenan"? Mummy ta ce "eh yarinya mai hankali da kunya da za ka bi maganata da ka nemeta, don daga gani ' yar gidan mutunci ce". Yace "Mum ba ki gane ba ne ni fa duk 'yan matan da ke zuwa gidan nan ba ni na ke cewa su zo ba,in fact wasu ban ma ta6a ganinsu ba, kuma har yanzu ban samu wadda na ke so ba, please Mum adaina takura ni akan wad'ancan ' yan matan wahala ce bata ishe su ba that's all". Da haka ya mik'e yana shirin tafiya Mummy ta ce "yanzu Abeed za ka so ' yan uwanka su Arfat su fad'a irin Wannan halin a fad'i irin abinda ka fad'a a kansu, don nasan yadda ka ke son su". Ya ce "no Mummy nasan ba za su yi irin wannan halin ba, Mummy ta ce" shi kenan dai, idan Daddynku ya dawo za mu tattauna akan maganar, je ka kawai".............. Mum Twins 😍 & Auntie M Jabo 🍃 M Twins😍& Auntie M. Jabo ✍🏾🍃 💫AN YI WALK'IYA 8💫 ©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo ®NWA K'arasawa ta yi in da Mufeeda ke tsaye kamar an dasata ta ce "mufy ya na ganki a tsaye, bayan ya tafi dama nasan ba lallai ya amince da buk'ata na ba". Cikin yak'e Mufeeda ta ce "kar ma ki yi wannan tunanin Fadeela, zai so ki da yardar Allah, yanzu ma don bai ganki ba ne na tabbatar idan ya yi ido hud'u dake ba abinda zai hana ya so ki". A jiyar zuciya Fadeela ta yi, sannan ta ce "ta yaya zan kuma had'uwa da shi bare har ya ganni?? Kar ki manta, ko sunansa ban sa ni ba, bare in da ya ke". Murmushi Mufeeda ta yi, ta ce " idan akan wannan ne ki kwantar da hankalinki kamar tsumma a randa, idan kullum kike son ganin Abeed za ki gan shi da yardar Allah." Cikin mamaki Fadeela ta ce "wow! nice name, sunansa kenan"? Mufeeda ta gyad'a kai alamar eh, Fadeela ta cigaba da fad'in "amma mufy ta yaya zan gan shi duk lokacin da na ke so ya gaya miki sunan unguwarsu ne, ko wurin aikinsa ?" Dariya Mufeeda ta yi sosai sannan ta ce" wannan kuma sai kin ba da wani abu sannan zan gaya miki, "6ata rai Fadeela ta yi cikin sigar wasa ta ce" dad'ina da ke kenan, yanzu za ki fara ja mun rai tunda kin ga ina son ji ". Tafiya Mufeeda ta fara tana cewa" shi kenan tunda ba kya son ji, da tuni kin mik'o wani abu, "gabanta Fadeela ta tara tare da cewa" haba friendy ko haka ki ka bar ni ai kin ja mun rai, don Allah ki gaya mun", ta k'arashe maganar kamar za ta yi kuka. Mufeeda ta ce "don't cry k'awata, he's my cousin", waro ido Fadeela ta yi tare da daka tsalle ta rungume Mufeeda tana cewa "don Allah da gaske kike yi mufy"? Mufeeda ta ce" yes da gaske ne ko gobe ki ke so zan kaiki gidansu ya Abeed, "Fadeela ta kuma k'ank'ameta tare da cewa amma na ji dad'i Allah ya sa hakan ya zama silar cikar burina." Mufeeda ta ce "ameen, sannan ta duba agogon wayarta ta ce" gaskiya Fadeela dare yayi fa, gashi lunching d'in an fara a makare bari na kira driver ya zo, sai ya fara kai ki gida, sannan sai mu wuce ". Fadeela ta ce" gaskiya kam don kar ayi mana fad'a kinsan hajiya idan ta fara," suka saka dariya. Www.hauwajabo.blogspot.com Www.jabohauwa.WordPress.com [4/11, 2:54 PM] : 💫AN YI WALK'IYA 12&13 💫 ©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo ®NWA Ana kiraye_kirayen sallar isha'i Daddy ya dawo, kaitsaye masallacin manne da gidan ya nufa domin sauke farali, bayan an idar da sallah tare suka fito da Abeed zuwa cikin gidan, suna tafe suna hirarsu irin ta d'a da uba, Mummy suka tarar a parlor ta na jiran k'arasowar mai gidan nata, cikin fara'a da girmamawa ta yi masa sannu da zuwa, tana fad'in "dama na ce yanzu haka masallaci ka wuce", Daddy ya ce "eh na shigo ana shirin ta da sallah na ce bari na yi sallar in yaso kawai na shigo gaba d'aya" ya fad'a yana murmushi Mummy ta ce "gaskiya kam, yanzu dai ga abinci nan an kammala kai kawai mu ke jira", ok, bari na je na watsa ruwa takun, Daddy ya fad'a ya na shirin barin wurin. Sai wurin 8:30 suka zauna cin abincin, bayan sun kammala ne kowa ya yi hani'an, don su Abeed har sun bar wurin, Mummy ke sanar da Daddy maganar Abeed, ta k'arashe maganar da cewa "gaskiya Alhaji ya kamata a d'auki mataki akan maganar Abeed, don yanzu kusan sa'anninsa duk sun yi aure, wasu har sun fara tara yara, amma shi shiru ko zancen auren ba ya yi, ni abinda ma ya fi damuna shine k'udirin da ya d'auka ya saka a zuciyarsa na lallai shi sai 'yar gidan hamshak'in mai kud'i zai aura, bayan da talaka da mai kud'i duk na Allah ne". Gyd'a kai Daddy ya yi, ya ce "haka ne, amma kin san abinda za a yi"? Mummy ta ce " a'a, ya ce "dama Alhaji Usman tun kwanakin baya yake maganar mu had'a Abeed aure da 'yar wajensa Hafat, na ce da shi sai na yi shawara da ke, da kuma shi Abeed d'in, don bana son na takura shi akan abinda baya so, shi yasa na ba shi dama duk tsawon wannan shekarun, amma tunda abun na shi haka ya zama, lallai_lallai ki gaya masa ya je ya ga yarinyar su daidaita kansu, tunda ai yasan gidan, don Alhaji Usman ba 6oyayyene ba a wurinsa." Mummy ta ce "Allah dai ya sa ya amince, don lamarin na Abeed sai addu'a", Daddy ya ce "da kakkausar murya za ki gaya masa ni na ce ya je, idan dai ban da k'uruciya yaran gidan Alhaji Usman mai za a nuna musu, suna da tarbiya ga hankali ga ilimi, amma shi ya tsaya neman k'yale_k'yalen duniya da ba zai anfaneshi da komai ba sai wahala". Mummy ta ce " wallahi kam, ai yaran yanzu ba sa gane abinda ake hango musu, sai abinda zuciyarsu ta raya musu shi suke yi, bayan bahaushe yace " son zuciya 6acinta". Daddy ya ce "sosai Allah dai yasa mu ga ne", mummy ta bi shi da ameen". ********* Tun da safe Abeed ya yi shirin zuwa office kamar yadda ya saba, duk safiya kafin ya wuce office sai ya je ya yiwa mummy sallama ita da Daddy in dai ya na gari ko bai yi sammakon fita ba. Bayan ya shiga mummy ke sanar da shi yanda suka yi da Ddynsa akan maganar neman auren 'yar gidan Alhaji Usman, zaro ido waje ya yi yana fad'in "Mum wai wani Alhaji Usman"? Mummy ta ce" akwai wani Alhaji Usman bayan aminin Daddyn ku"? Mere baki gefe ya yi, sannan ya ce "Mum mun San fa komai gameda Alhaji Usman kawai dai muna shiru ne." Fito da ido waje ta yi, ta ce" mai ka sa ni game da shi? yana da wani mugun Hali ne"? Abeed ya ce "no ba abinda na ke nufi ba kenan, kawai dai a takaice yaron Daddy ne, don dai Daddy ya taimaka masa ya ba shi companyn sa da ke bompai ne ya na kula da shi, shi ne kawai ake ganinsa wani mai arzik'i, kin ga kuwa Mum kamar ni haka, ta yaya zan auri 'yar yaron babana!!! Ai na ci baya sosai, gaskiya mum bazan ma iya ba." Mummy da tunda ya fara magana take tafa hannu tana sallati tace "yanzu Abeed tanan ka 6ullo kuma"? Ya ce " Mummy don dai kin san Daddy da rik'on abokanai ne na tun k'uruciya amma ba don haka ba, ina laifin ko a cikin manya_manya attajiran garin nan ya nema mun 'yar wani perhaps da na amince na yi manage da ita." Mummy kam tuni ta dask'are a gurin don mamaki, tace "au maneji ma za ka yi da ita"? To bari Alhaji ya dawo na gaya masa, gaskiya ya nemo mai ruk'iyya ya duba ka don ina ga ba zaka rasa jinnu ba". Dariya sosai Abeed ya yi sannan ya ce "Mum wallahi ras na ke, kawai dai na gaya miki abinda ke zuciya ta ne," sai kuma ya kalle agogon dake daure a hannunsa ya Ce "Mum gaskiya na makara bari na tafi sai na dawo," Mummy tace "Allah ya kiyaye hanya", yace "ameen tare da ficewa daga d'akin...................... Mum Twins 😍 & Auntie M Jabo 🍃 [4/11💫AN YI WALK'IYA 9💫 ©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo ®NWA Cikin 6acin rai Abeed ya koma gida, parking kawai ya yi ko kulle motar bai yi ba, ya wuce part d'in sa, ransa a dagule yake gaba d'aya, yana tunanin wai yaushe ne burinsa zai ciki, ya samu yarinyar da ta dace da shi, wacce ya ke mafarkin samu, domin shi kansa yanzu ya hak'ik'an ce da ya na buk'atar aure, amma matsalar duk 'yan matan da ke sonsa yanzu ya raina arzikin iyayensu, duk da cikin su babu wadda za a d'auka ace babanta matsiyaci ne, don dai shi ya d'auki k'atoton buri ya sakawa zuciyarsa, dole sai 'yar mai hannu da shuni, lokaci d'aya ya tuna da wacce akace tanasonsa, wai babanta yayi rik'on logal government, dai rainin wayo, wani dogon tsaki yaja, yadan juya kwanciyar sa, ya kalli a gogon d'akin yana lumshe ido. ********* Goggo wacce nake tunanin y'ar uwar Dadyn su Abeed ce, zaune take tareda Mumy suna hira, Abeed ne ya shigo ya gaishesu cikin sakin fuska sannan ya wuce d'akin sa, nan suka fara hirar yau da kullum, har Goggo ta gangaro akan abinda ya dad'e yana damun ta, "hajiya yaran yanzu sai a hankali, sam basa tunani basa naziri, yanzu za ku ga wasu yaran masu kud'i idan za su yi aure sai su rik'a hangen wadda mahaifin ta ya dame nasu ya shanye da naira, don zilama, maimakon su nemi dai_dai su, tunda Malam bahaushe ma ya ce "dai_dai ruwa dai_dai tsaki, kuma kowace k'warya da abokin burminta" sannan ma ina laifin su yi k'asa_k'asa su nemi 'yar talaka bawan Allah suma su samu su lasa, kinga ai an taimaki juna an rufawa juna asiri ta wannan hanyar, amma ba a yi saboda buri ya cikawa masu irin wannan halin zuciya, kowa sai dai-dai shi," Mumy tace "Wallhy zancen ki dutse Goggon yara, nima abin yana damuna, musamman idan naga halin yaronnan banajin dad'i sam, amma kinsan kosu talakawan akwai nasu sabida sai su k'wallafa dogon buri wa yaran su, su mayar da yayan nasu kamar jari, domin wasu sai ka ga sun zaune jiran mai d'an maik'o_maik'o har yarinya ta tsofe a gida, ba iyayenba ba ' ya'yan ba, kije gida ki rasa gane uwa da yaran gida, akwai wani gida da mukaje ta'aziya, a gidan naga mata 'yar kyakyawa, wacce nake tunanin zata haifi yara biyu ko uku, nake tambayar matar gidan, an mata amarya ne, dan tare na gansu, sai take cemin ai 'yar kice wance, wallhy saida na kai zaunedDan mamaki, na tuna yarinyar sa'ar Muhammad ce fa! Amma har yanzu tana gida," Goggo ta saka dariya, " kin bani dariya, wai an miki amarya ne" itama Mumy dariyar tayi suka ci gaba da hira" wannan zamanin kowa kwad'ayi ya yi masa yawa, bayan sun mata Allah ke yin komai, domin kowa an riga an rubuta k'addararsa tun kafin ya zo duniyannan, we just trace, sai ka ga budurwa ta zauna jiran Mr right har ta tsofe tun tana samun masu zuwa har lokacin ta ya wuce ya zamana bata samu, ta tashi a tutar babu, k'arshe sai ta auri wanda bataso, sabida da yawa masu wannan burin, wallhy basa auren mazan da zuciyar su takeso, saidai dan kud'i, su tashi ba wan ba k'ani, ta yi haihuwar guzuma 'ya kwance uwa kwance, ba mai d'an maik'o_maik'o ba mijin kwatakwata" nan ma saida suka dara, Goggo tace, " nifa kina magana kina saka engilishi, kuma kinsan ba ganewa nakeyiba," sukayi dariya gaba dayan su, Goggo tace, " Allah ya sa masu wannan halin su gano su bari dan ba alkhairi acikinsa" ameen Mumy ta amsa dashi, Na kalli M Twins nace "nifa al'amarin Abeed yana bani mamaki domin ya d'ebo da zafi, kace sai 'yar wane ko wane," M. Twins tace " ?kedai bari Aunty Jabo, Allah na d'auka irin wannan abin matane kawai keda wannan hali, ashe har maza ma sunayi, abin kunya, amma hausawa sun ce "kowa ya d'ebo da zafi bakinsa"..........." Www.hauwajabo.blogspot.com Www.jabohauwa.WordPress.com M Twins 😍 & Auntie M. Jabo ✍🏾🍃 [4/11, 2:54 PM]💫AN YI WALK'IYA 14&15 💫 ©Mrs Saif & Hauwa M Jabo ®NWA Daddy na dawowa Mummy ta kwashe yanda suka yi da Abeed ta fad'a masa, ai kuwa ya yi ta fad'a, nan take ya d'auki waya yace "da Abeed duk abinda ya ke yi ya ajiye ya zo yana kiransa", Abeed ya ce "to Daddy ga ni nan zuwa" don dama ya san sai an yi haka, cikin abinda bai fi 10 minutes ba ya shigo gidan, kaitsaye parlourn Daddy ya nufa, bayan ya gaishe su, Daddy ya fara magana "Abeed ka saurare ni ka ji abinda zan gaya Maka, domin maryam ta gaya mun duk yanda ku ka yi da ita, to bari ka ji bazan d'auki wannan shashancin ba, dole ka bi maganata idan ba haka ba, ka sanni sarai". Rausayar da kai Abeed ya yi ya ce "Daddy dama abinda ya............" dakatar da shi Daddy ya yi ta hanyar d'aga masa hannu, yace "ba na son jin wata magana yanzu kawai tashi ka je ka yi abinda na saka ka". Jiki a sanyaye Abeed ya tashi yana fad'in "to". Daga nan dakinsa ya wuce, amma zuciyarsa a cunkushe take yana tunanin meye mafita, don dai shi ya hak'ik'ancewa zuciyarsa ba zai ta6a auren 'yar gidan Alhaji usman ba, ya san kwata_kwata ba ajinsa ba ce, da wannan sak'e_sak'en har barci ya yi awon gaba da shi. Ko da ya tashi da safe fuskar nan tasa ba annuri, su Arfat ma da suka ga yanayinsa tuni suka kama kan su, tare da gimtse dariyar da ke cin su, domin mummy ta gaya musu duk abinda ake ciki, bayan ya fita ne Arfat ta kalli Afrat ta ce "ni wallahi gwanda da Daddy ya yi wa ya Abeed haka ko ya maida hankali ya yi auren, mu ma mu fara ganin babies a gidanmu". Afrat ta ce "ni kuma gani na yi da Daddy ya kyale shi ya za6a da kan sa, idan ya ga bai samu wadda ya ke so ba ai dole ya yi hak'uri ya auri wata,kuma ni yaran gidan Alhaji Usman ba su yi mun ba, sai gwalli da iyayi amma ba su da wani kyau". Murmushi Arfat ta yi sannan ta ce "Ai k'arshen mai ruwan ido ke nan". Bayan ya dawo daga aiki mummy ta takurashi akan ya je su gana da Hafsat, dole ba yanda ya iya ya yi shirin zuwa gidan Alhaji Usman. Duk da ya saba shiga har cikin gidan a duk lokacin da ya je, amma wannan zuwan da ya yi tsayawa ya yi a inda ya yi parking motarsa, sai da mai gadin gidan ya ga ba shi da niyyar shiga ciki don ya ga ya dade a tsaye sannan ya je ya ce da shi, "yalla6ai Alhajin ya na ciki ka k'arasa mana", juyawa ya yi ya kalleshi ya ce "ai ba wurinsa na zo ba, ka je ka ce ana kiran Hafsat" Mai gadi ya ce "to bari na je na gaya mata" bai fi minti biyu da tafiya ba, ya dawo ya ce "ta ce tana zuwa". Hafsat kuwa tunda mai gadi ya sanarda ita ana sallama da ita, ta tambaye shi waye ya ce da ita Abeed ne, ta shiga tsallen murna, dama ba ta dad'e da fitowa daga wanka ba, nan da nan ta hau kwalliya a fenta can a manna can har ta gama, ta fito cas da ita. Dama mai gadi ya gaya mata yana bakin gate so direct can ta nufa, ana tafe ana yauk'i, kamar ba za a taka ba, sai kuma jikinta ya yi sanyi lokacin da ta fara hangoshi, don yanayinsa ya fi kama da wanda aka aikowa sak'on mutuwa, sai ta fara tunanin ko wani mugun sako ya kawo mata ne! Daurewa ta yi ta k'arasa inda ya ke ta masa sallama tare da fad'in "sannu da zuwa", sallamar kawai ya amsa ya yi shiru, sun yi kusan 4 minutes ba wanda ya k'ara cewa komai, sai can Hafsat ta ce "ai da ka zo mun k'arasa ciki ko"? A'a kawai ya ce da ita, ta ce" ai tsayuwar ce ba dad'i, ko za ka zo mu koma daga can wurin ta yi nuni da wani wuri d'an nesa da su kad'an da aka sawa rumfa tare da resting chairs, ya ce "ba zama zan yi ba, don yanzu haka bai fi 5 minutes na tafi ba", Hafsat a ranta ta ce anya kuwa Abeed ya na sonta? wata zuciyar ta ba ta amsa da cewa ai da yana sonki da tunda kika zo kin gani a fuskarsa, kawai dai........... Abeed ne ya katse mata tunani ta hanyar yin magana, yace "ba sai na miki dogon bayani, don na San a gida an miki bayanin komai, duk da dai ke ban san tunaninki akaina ba, amma ni zan gaya miki gaskiyar abinda ke zuciya ta, ni ban yarda da wannan auren had'in ba, kuma ba zan iya bijirewa maganarsu ba, kuma ke kin san duk burin mace bai wuce ta samu miji mai sonta da kaunarta ba sannan yake kuma tausayinta ba, don shi ne a kowane irin hali zai kasance tare da ita, idan dai ki na buk'atar hakan to kada ki kuskura ki amince da aurena, shawara ce na ke ba ki idan ki d'auka kin taimaki kan ki, idan kuma ba haka ba a shirye na ke da d'aukan duk wani k'alubale sannan zan aureki, smma zaki rasa duk wayanchan abubuwan idan kin shirya bismillah!!". Bai jira abinda za ta ce ba, ya fad'a mota ya yi mata key ya fice daga gidan. Hafsat kuwa ta fi k'arfin 10 minutes a tsaye a wurin tana maimaita kalamansa, sai da ta ga hakan ba mafita ba ne ta shuri k'afafuwanta ta shige ciki............. Mum Twins 😍 & Auntie M Jabo 🍃 [4/11, 2:54 PM] 💫AN YI WALK'IYA 6&7 💫 ©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo ®NWA Tun da safiyar ranar mubarak yake ma Abeed waya akan kada ya manta please, yamai SMS ba adadi, k'arshe ya yarda zai tafi, dan har ya shirya dojewa. Sai wurin k'arfe tara da minti ashirin da biyar Abeed da tawagarsa suka shiga hall d'in, cikin takun isa da k'asaita yake tafiya, ya rufe idonsa da wani shade bak'i kaitsaye gurin da aka tanada domin zaman su suka nufa. Wohoho! Ku zo ku ga 'yan mata yanda suka zuba masa na mujiya suna kallo, kai basu kad'ai ba har mazan dake gurin kallonsa suke yi tamkar sun ga wata sabuwar halitta, shi kuwa gogan naku ko kallo ba su ishe shi ba, tafiyarsa kawai yake cikin isa da izza har ya isa wurin zaman su. Tun shigowarsa wata yarinya mai amsa sunan Fadeela, muka ga duk ta rud'e ta rikice, sai wani dube_dube take kamar mai neman wani abu. Sai can kuma muka ga ta nufi wani side na musamman, domin an yi decorating gurin sosai fiye da inda take zaune, Da sauri ta k'arasa wurin har tana tuntu6e, tare da rik'o hannun wata budurwa wadda ba zata wuce sa'arta ba, sannnan ta ce "Mufy ta so don Allah ki gan shi shine wanda na ke yawan yi miki maganarsa" ido Mufeeda ta zuba mata na d'an lokaci sannnan ta ce" wai ki na nufin guy d'in da ba ki da aiki sai na maganarsa shine ya zo nan gurin,"? Fadeela ta ce "eh tare da langa6ar da kanta gefe," Mufeeda ta yi farr da ido,sannnan ta ce "gaskiya fady kin ban kunya, duk yanda kika h'adun nan, kuma kike gwara kan samari son ranki amma ki 6ige da baran soyayya akan saurayin da ko sunansa ba ki sa ni ba". Dafa kafad'arta Fadeela ta yi tare da cewa "friendy ba ki ga guy d'in ba ne that's why kike wannan maganar, kin san first class guy, full options to shi ne, ni tsoro ma nake kar ki gan shi ki kasa controlling kan ki ki je ki shigar da kan ki ba ni ba" ta k'arashe maganar tare da sakin dariya! Duka Mufeeda ta kai mata, ta goce sannnan ta ce "an gaya miki akwai wanda ya isa ya ture gwamnatin k'albina ne," Mufeeda ta cigaba da fad'in "ni dai zo ki nuna mun in da ya ke, ga ganshi, na cigaba da abinda na ke yi". Fadeela ta ce "na ga dai sun nufi wurin da aka tanada don manya_manya abokan ango" ta fad'a tana d'an kalle-kalle OK, "to ta yaya zan yi na gane shi??" Cewar Mufeeda, nari mu je na nuna miki shi ko daga nesa ne, d'an nesa da su Fadeela ta tsaya take nunawa Mufeeda shi, ba tare da ko na kusa da su sun gane abinda suke yi ba. Tun da Mufeeda ta hangoshi take wasiwasin wani abu a zuciyarta, sai da ta zo daf da shi sannan ta tabbatar da abinda take zato. Sallama ta yi sannan ta ce "sannu yaya Abeed" Jin an kira shi da yaya, ya tilasta masa d'agowa da kan sa domin ganin mai magana. Fuskarsa ya d'an saki sannan ya ce " yawwa sannunki", ta cigaba da fad'in ashe kai ma ka zo bikin k'awarmu"?? Jin bai ce komai, ta ce "angon ne abokinka ke nan"?? kai ya gyad'a mata kawai, ta ce" ai ni amaryar ce close friend d'ina". Jin ya kuma shiru ta ce "yaya ba ka son zuwa gidanmu su Arfat ne kawai ke zuwa". Hmm! kawai ya ce, nan ma shiru ne ya kuma ratsawa, sai da ta ga shirun yayi yawa ta ce "dama akwai maganar da ta kawoni wurinka idan ba za ka damu ba ka ba ni 5 minute's please", kamar ba zai yi magana ba, sai can ya mik'e ya yi mata nuni da su fita daga gurin. Gefe suka koma, sannan ta fara masa bayanin abinda ya kawota, ta k'arashe maganarta da cewa don Allah yaya ka taimakawa k'awata ba ka ga yadda ta ke sonka ba." Bud'ar bakinsa sai ya ce "waye mahaifinta"? Cikin rashin fahimtar maganarsa Mufeeda da ta ce" Babanta dai d'an siyasa ne", ya ce "muk'amin meye da shi"? eh, to ni dai abinda na sa ni ya ta6a rik'on k'warya a local government". "What!" ya fad'a da k'arfi, yana had'e fuska, daga haka bai k'ara cewa da ita komai ba, sai ga ni ta yi yana niyyar fita daga hall d'in ba ki d'aya. Da sauri ita ma ta bi bayansa,bayan ya isa in da ya ajiye motarsa yana k'ok'arin shiga, ta sha gabansa tana fad'in "haba yaya Abeed ba ka ce komai ba, ba ka ga yanda yarinyar take mutuwar sonka ba". Ai kuwa sai dai ta mutu in dai ni ne, I hate her, ya fad'a tare da shigewa mota ya ja da k'arfi da niyyar ficewa daga wurin, dai_dai lokacin Fadeela ta fito.......................... Www.hauwajabo.blogspot.com Www.jabohauwa.WordPress.com M Twins 😍 & Auntie M.Jabo ✍🏾🍃 [4/11, 2:54 PM] 💫AN YI WALK'IYA 10&11 💫 ©Mrs Saif & Hauwa M Jabo ®NWA Bayan kwana uku Mufeeda da Fadeela suka yi shirin zuwa gidansu Abeed don gaishe da Mumy, sun taki sa a kuwa don sun tarar da Arfat da afrat suna gida, su na yin sallama, Arfat ta taso da sauri ta rungume Mufeeda tana fad'in "oyoyo! Mufeeda yau a gidanmu" ? Kafin ta yi magana, Mumy ta fito, nan da nan ita da Fadeela suka zube su na gaisheta, cikin fara'a Mummy ta amsa musu, sannan ta ce "Mufeeda shiru kwana biyu kin daina lek'o mu". Mufeeda ta ce "eh wallhy Mummy school ne ya 6oyeni", mummy ta ce " ayya!, nima nasan Mufeeda akwai zumunci, to Allah ya ba da sa a", suka ce ameen ". Sai kuma ta kalli Fadeela ta ce da Mufeeda" Wannan k'awarki ce "? Murmushi Mufeeda ta yi tana kallon Fadeela ta ce" eh, Mummy k'awa ta ce " Allah sarki ya sunanta"? Tace" Fadeela ", sannu Fadeela Mummy ta fad'a tare da mik'ewa ta na cewa" Arfat haka za ku bar bak'in naku ba d'an abun ta6awa "? Afrat ta ce" Mummy dama yanzu na ke son tashi", ya dai kamata Mummy ta fad'a tare da shigewa kitchen. Sun sha hira sosai, sannan daga bisani Mufeeda take ce da Arfat ya Abeed na nan kuwa?? Arfat ta ce "a'a, ina za ki ga ya Abeed yanzu, ai sai wurin k'arfe biyar yake dawowa daga office". Mufeeda ta ce "ok, Arfat ta ce" ko ta samu ne "ta fad'a tana murmushi, ita ma Mufeeda murmushin ta yi, sannan ta ce "sosai kuwa, Fadeela ce ke masifar son ya Abeed," Arfat ta ce "wow! ai kuwa ina ganin Fadeela na ji ta kwanta mun a rai, Allah ya sa ya Abeed ya amince, gaskiya da ya yi mata". Sai kuma ta mik'e da sauri ta na fad'in bari na je na sanarda Mummy ta zo ga sirikarta", Fadeela ta hanzarinta ta rik'o hannun Arfat tana Murmushi ta ce "don Allah kar ki gaya mata yanzu bari sai mun tafi Allah kunya nake ji, ita kanta Mufy ta san ba halina ba ne cewa ina son wani kawai na d'auki son yayanki a wani 6angare na k'addarata, amma kwata_kwata mace ta ce tana son namiji baya burgeni", ta k'arashe maganarta da d'an guntun hawaye. Dukan su jikinsu ya yi sanyi Arfat ta ce "in dai mummy ce ba ta da matsala Allah ki daina ma Jin kunya don ta saba ganin 'yan mata kala_kala masu zuwa neman ya Abeed". Har wurin k'arfe shida Abeed bai dawo ba, don haka suka yi shirin komawa gida, mummy ta had'a musu sha tara ta arziki, sannan ta saka driver ya kai su gida. Sai wurin k'arfe bakwai ya shigo gidan , bayan ya yi wanka ya ci abinci, mummy ta same shi tace ta na son yin magana da shi. Murmushin gefen kumatu ya yi sannan ya ce "ina Jin ki Mum". Mummy ta fara magana "Abeed dama akan maganar aurenka ne, gaskiya ya kamata ka nutsu kasan mai kake yi zuwa yanzu, ka ajiye duk wani shirme da ke ranka, ka za6i matar aure ka yi aurenka ya fiye maka, kuma mu ma zamu fi samun kwanciyar hankali, don na gaji da zaryar da 'yan mata ke mana a cikin gidan nan". Juyo da dubansa ya yi sosai gareta, sannan ya ce "Mum yau ma wata ta zo kenan"? Mummy ta ce "eh yarinya mai hankali da kunya da za ka bi maganata da ka nemeta, don daga gani ' yar gidan mutunci ce". Yace "Mum ba ki gane ba ne ni fa duk 'yan matan da ke zuwa gidan nan ba ni na ke cewa su zo ba,in fact wasu ban ma ta6a ganinsu ba, kuma har yanzu ban samu wadda na ke so ba, please Mum adaina takura ni akan wad'ancan ' yan matan wahala ce bata ishe su ba that's all". Da haka ya mik'e yana shirin tafiya Mummy ta ce "yanzu Abeed za ka so ' yan uwanka su Arfat su fad'a irin Wannan halin a fad'i irin abinda ka fad'a a kansu, don nasan yadda ka ke son su". Ya ce "no Mummy nasan ba za su yi irin wannan halin ba, Mummy ta ce" shi kenan dai, idan Daddynku ya dawo za mu tattauna akan maganar, je ka kawai".............. Mum Twins 😍 & Auntie M Jabo 🍃 [4/11, 2:54 PM] 💫AN YI WALK'IYA 21&22💫 ©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo ®NWA Haka kuwa aka yi, don bayan teema Daddy ya nemawa Abeed auren 'yan mata sun kai uku, duka' ya' yan abokan sa ne , amma yanda ta kasance da sauran suma haka takasance da su, don duk a cikinsu bai katarin samun yarinyar da ya ke mafarkin aura ba, don haka bai yi k'asa a guiwa ba, wajen neman mafita ba, d'aya bayan d'aya sai da ya nemi hanyar rabuwa dasu. Daddy kuwa ransa ya kai k'ololuwar 6aci, don Abeed ya kunya ta shi a idon abokan sa, kuma ya watsa masa k'asa a ido, yanzu haka yana cikin fushi da shi, kuma har yanzu yana nan akan bakansa, na sai an yi auren kafin lokacin da ya ce ya cika. Yau kamar had'in baki, Mrs Saif dani M Jabo duk mun makara zuwa gidansu Abeed don d'auko muku rahoto, sai after 10pm muka isa gidan, kaitsaye babban parlourn gidan muka nufa, sai dai wayam ba kowa a ciki, said k'arar A.C da kuma T V da ke ta 6a6atu ita kadai, ni kam d'aya daga cikin kujerun dake parlourn na samu na zauna, na juyo da dubana in da Jabo ke tsaye, na ce "Anya Auntie jabo yau za mu samu wani labari kuwa"? Jabo ta ce "ni ma abinda na ke tunani ke nan maman Twins, kalli fa hatta 'yan aikin dake saraftu ko yaushe ba kowa duk sun shige, ko motsin su ba a ji." Na ce "ko dai d'aki za mu bi su ne kawai"? Jabo ta ce "haka ma za mu yi, maybe baza mu rasa wani abu acan ba, nan da nan kuwa na mik'e, muka nufi d'akin Abeed, ko da muka shiga mun tarar ya baje a lafiyayyen gadonsa sai sharar barci sa yake yi, adole muka fito daga d'akin, tunda babu abun rubutu a nan, d'akin su Arfat muka nufa daga nan, sai dai suma duk maganar d'aya ce, don kuwa suma sharar barcinsu suke yi hankali kwance, bayan mun fito daga d'akin su afrat, Jabo ke cewa "ni kuwa Mrs Saif lafiya mutanen gidan nan yau suka yi barci da wuri haka"? Na ce "hmm! Ke ma ke fad'a kin riga ni fad'a ne kawai, amma nima tunanin da na ke yi ke nan, amma bari mu koma part d'in Mummy mu gani ko akwai wani abun d'aukowa a can". Side d'in mummy muka nufa gadan_gadan, parlor muka fara shiga, ba kowa, daga nan muka sulale muka fad'a bedroom d'in ta, nan ma shiru ba kowa, sai muka yi zaton ko tana toilet ne, muka d'an saurara amma ba mu ji alamar mutum a ciki ba , almost 10mnts muna tsaye muna jiran fitowar Mummy ammma shiru, har sai da muka tabbatar wa kanmu cewa Mummy bata part d'in ta kwata_kwata. Ni kam Mrs Saif har na fara tsorata, na juya na cewa "Jabo gaskiya gidan nan ba lafiya ba". Auntie jabo tace "Nima abun ya d'aure mun kai, amma idan ba lafiya ba, ta yaya su Abeed za suna sharar barci irin haka"? Na ce "Da haka kuma, nima ga shi har na fara Jin barci,gaskiya mu je kawai gobe ma dawo, M Jabo tace "ni kaina barcin na ke ji". Har mun fito, da niyyar tafiya sai muka ji kamar sautin kukan Mummy yana tashi daga part d'in Daddy, kasancewar ba nisa tsakaninsu, inkiya Jabo ta yi mun akan na k'araso na ji kunsan Jabo ba Dama wajen jin kwakwaf, sai da na matsa daf da windown da ke d'akin na tabbatar da Mummy ce ke shar6ar kuka, kallon_kallo muka tsaya yi, muna tunanin mai ya saka Mummy kuka irin haka, a cikin Daren nan, maganar Daddy ce ta katse mana tunani, don son Jin abinda ya ke fad'a ba mu San lokacin da muka fad'a parlourn ba, Allah ya so suna cikin d'aki, da asirin mu ya tonu. Abinda muka ji Daddy na fad'a ne, ya tilasta mana saka hannayen mu akan bakunan mu, kada mu yi baran 6aramar fitar da sauti har su an kara da mu a wajen. Mummy muka jiyo tana yiwa Daddy magiya akan ya hak'ura da maganar, koda Abeed zai tabbata bai yi aure ba, Daddy ne ya fara magana a hassle ya ce "kin ga maryam, maganar nan dole a fade ta, don komai lokaci ne, kuma ita magana lokacin fita ne da ita, idan lokacin fitar ta ya yi, dole ta fita." Mummy muka hango ta yi baya ta zauna sharaf, mu ma muna ganin haka, muka tattara inamu inamu muka yi waje. Bayan mun fito ne muke tattauna girman maganar da muka ji su Daddy na yi, Auntie jabo ce ta ce "gaskiya Mum Twins maganar nan ta d'aure mun kai," na ce "Ai ba ke kadai ba, nifa da ba tare muke ba da sai nace ba daidai naji ba, ni kai na burina bai wuce Allah ya kai mu gobe ba, mu zo mu ji yanda maganar take dalla_dalla ba," M Jabo ta ce "Ai ni ji na ke yi kamar yau na kwana a gidan nan, don kar mu makara zuwa," na ce "Ai kam dai. Kuma readers sai ku biyo mu don Jin abinda za faru..... Mum Twins 😍 & Auntie M. Jabo 🍃 💫AN YI WALK'IYA 💫 ©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo ®NWA K'arfe bakwan safe a gidansu Abeed ta yi mana, ko da muka shiga gidan suna ta hada_hadar had'a breakfast, kasancewar ta weekend, Arfat da Afrat muka hango a kitchen suna ta faman aiki, tare da 'yan aikin gidan, don mummy ta riga ta sabar musu da aiki musamman girki don duk ranar da ba school tare suke shiga kitchen har Mummy. Arfat ce ke wanke hannunta a jikin sink, afrat ta je ta ce da ita "ya Arfat na ga har yanzu mummy bata fito ba, ko lafiya "? Arfat ta ce "Yanzu nima na ke shirin dubata, ki cigaba da duba girkin bari na je, na dawo". Afrat ta ce "to " Sallama Arfat ta ke ta kwad'awa tunda ta shiga parlourn Mummy, har ta K'arasa bedroom, sannan ta jiyo muryar Mummy tana amsawa kasa_kasa, da sauri Arfat ta K'arasa kan gadon ta yaye bargon da Mummym ta kudundune a ciki, tana fad'in "Mum lafiya,?" Cikin raunananniyar murya Mummy ta ce "lafiya lau" Arfat ta ce "Amma shine Mummy ba ki fito ba tun dazu"? Mummy ta ce "jikin ne yau bana Jin dadin sa, amma je ki ga ni nan zuwa". Jiki a sanyaye Arfat ta ce "to mummy sai kin fito," tare da Jan k'ofar d'akin. Amma a can k'asan zuciyarta tana tunanin mai ya samu Mummyn su don ba ta saba ganinta a irin wannan yanayin ba. Bayan sun kammala breakfast ne Daddy ya ce su zauna dukan su yana da magana, Mummy kuwa da tun shigowarta, ta kasa sakewa don ko abincin kirki bata ci ba, haka su Arfat ba su iya tsayawa sun ci abincin ba kamar yadda suka saba, saboda don duk sun takura ganin halin da Mummyn su ke ciki. Daddy ne ya yi gyaran murya ya fara magana da cewa "Muhammad!" Yanayin yadda ya fad'i sunan ya saka Abeed saurin juyawa ya ce "Na'am," wadda sautin ta bai fita ba, don ko Arfat dake zaune kusa da shi bata san ya fad'a ba. Daddy ya cigaba da fad'in "Tunda abin na ka ya zo da haka, ka riga kasan alkawarin da na yi akan aurenka, kuma kasan ba zan ta6a warware shi ba, don haka muka yanke shawara ni da mahaifiyarku akan za mu had'a aurenka kai da 'yar uwarka Arfat,......!!!" Tashin hankali muka gano a idanunsa k'arara, don kuwa ba Abeed ba har Arfat ta shiga rudani, don wata zabura ta yi, wadda ta yi dai_dai da tashin Abeed, hakan ya haddasa gwaruwar kawunansu, lokaci d'aya suka yi baya, kowa dafe da kan sa. Ita kuwa Mummy wasu zafafan hawaye ne, suka biyo kumatunta, don tasan a rina. Abeed ne ya yi k'arfin halin cewa "Dad ban gane mai ka ke nufi ba?, ka fahimtar da ni, Dad ko ka manta we are the same blood, if am not wrong, Arfat ita ke bina fa. sannan nan k'aramar k'anwar mu Afrat". Arfat kuwa da gudu ta je, ta fad'a jikin Mummy tana kuka, ta ce "Mummy ban ga ne abinda Daddy ya ke fad'a ba, how comes zan auri yayana, the same Mum & Dad fa, ban ta6a ji ba, ko a lokacin jahilan farko ba,....!!!" Wata iriyar tsawa Daddy ya daka mata tare da cewa "Me kike nufi?, kin fi ni sanin abinda ya kamata na yi ne?? " Mummy ce ta ce "Alhaji sanin kan ka ne, idan yaran nan suka ji wannan maganar sai sun dimauce har su kasa controlling kan su, don haka hak'uri za ka yi abi komai a hankali." Mikewa Daddy ya yi tare da nuna Abeed da hannu ya ce "Kai ka jawo duk abinda ya faru , don haka ka shirya d'aukan duk abinda ya biyo baya." Daga haka bai kuma cewa komai ba ya fice daga parlourn. Abeed K'arasawa ya yi gurin da Mummy ke zaune ya ce "Mum sai yanzu zuciyata ta fara hasko mun, abinda tun d'azu na kasa ganewa, tabbas na fuskanci akwai wani B'OYAYYEN AL'AMIRI (Bebeelo ) da ya shafe mu, amma ba ku sanar da mu ba, don Allah Mummy ki fad'a mana mai ya ke shirin faruwa da mu ne"?? Mummy kam ba ta san lokacin da ta rushe da wani irin kuka ba, dama tun d'azu take rike shi, gaba d'ayansu rungume Mummym suka yi, suna rarrashinta ,, duk da Arfat da afrat suma kukan suke yi. Arfat ce ta d'ago da kanta ta fara magana cikin kuka ta ce "Mummy gaskiyar ya Abeed, don ni kaina na fara wannan tunanin, ko ma miye Mummy gwanda ku gaya mana, akan ku bar mu cikin duhu." Dakyar mummy ta samu ta tsaida kukan da take yi, ta ce "ku yi hak'uri 'ya'yana, za ku ji komai, tunda har Alhaji ya taso da maganar nan, tabbas na san zai gaya muku duk abinda ya faru, don haka ku kara hak'uri zuwa an jima za mu k'ara wani zaman". Ba don ransu ya so ba suka amince, kowa ya tashi ya nufi nasa guri zuciyoyinsu cunkushe da tunani kala_kala........ Mum Twins 😍& Auntie M Jabo 🍃 [4/11, 2:54 PM] 💫AN YI WALK'IYA 16&17 💫 ©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo ®NWA Adaidai k'ofar shiga parlourn su ta tsaya don daidaita natsuwarta, don kar a gane yanayin da take ciki, sabida lokacin da zata fito tana ta gwalli da iyayi, a dole ga matar Abeed, bayan tasan tana da 'yan adawa don akwai stepsisters d'in da suke sa'anni, kuma kowacce ta so ace ita Abeed zai aura, amma sai Abbansu ya ce hafsat aka ba shi, don haka tasan idan suka san yadda ta kasance musu da Abeed lallai za su yi mata dariya, ai kuwa tana shiga kaitsaye d'akinsu ta wuce, ta fad'a gado sharaf, tana tunanin mafita don gaskiya tana son Abeed, domin tasan idan ta yi nasarar aurensa ta more miji kuma ta tsere sa'a. Amma da ta tuna kalamansa sai jikinta ya yi sanyi, wannan shi ake kira ga k'oshi ga kwanan yunwa. ******** Abeed kuwa bayan ya koma gida, wanka ya yi sannan ya ci abinci, ya yi shirin kwanciya barci, a sannan ne yake tariyar abinda ya faru tsakanin sa da hafsat, tsaki ya ja, sannan ya ce "idan ban da abun Daddy ta yaya waccen yarinyar zata had'a kan ta da ni, ai kwata_kwats ba aji na ba ce" ni da na fison mace natural beauty, amma ga shi ita duk kyan na ta artificial ne, amma haka ga ni ta ke yi ta had'u, ba ta san ni ganinta na ke yi kamar wata horror ba," ya kuma Jan wani tsakin, tare da rarumo pillown sa ya k'ak'ume da niyyar fara barci, nan da nan kuwa ya lula duniyar masu barci, mu kuma mu ka ja masa k'ofa muka fice daga d'akin. Kusan 6 weeks da zuwan Abeed gidansu Hafsat, amma ko da wasa bai kuma lek'awa ba, kullum da uzirin da ya ke bawa Mummy idan ta yi masa maganar, har ta gaji ta saka masa ido. Hafsat kuwa kullum sai ta kirashi, shi kuma ya yi ta mata wulak'anci da cin fuska, daga k'arshe ma sai ta daina samunsa, don karya sim card d'in ya yi , ya chanza wani, don karya layi a gurin Abeed ba wani abu ba ne, halinsa ne ya saba haka tuntuni, da ga ya yarinya za ta takurashi da kira zai chanza wani layin. Hafsat tun abun baya damunta har ya fara damunta, don har 'yar rama ta yi, ga shi ta kasa gayawa kowa maganar har ummansu......... Auntie M Jabo 🍃& Maman Twins💫AN YI WALK'IYA 17&18 💫 ©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo ®NWA A kwance ta ke a d'aki tana aikin na ta, na neman mafita, kwatsam ta jiyo muryar babbar aminiyarta, Safiyya tana kwad'a sallama, a hanzarce ta mik'e ta rungumeta tana fad'in k'awata yau a gari? Kamar kin san ina neman ki, don da gobe na ke sa ran zuwa gidanku". Murmushi Safiyya ta yi ta ce "kamar da gaske"? Hafsat ta ce" wallahi da gaske na ke yi, domin akwai wata muhimmiyyar magana da na ke son gaya miki ki ba ni shawara". Safiyya ta ce "ok, to gaya mun ina Jin ki, tunda ga ni na zo", nan da nan Hafsat ta juyewa Safiyya abinda ya faru tsakanin ta da Abeed, a jiyar zuciya Safiyya ta sauke, sannan ta ce "Hafsat shawara kike so na ba ki ko? Hafsat ta ce eh" Safiyya ta cigaba da fad'in "kin san ita gaskiya d'aya ce tak, kuma d'aci ne da ita, i hope idan na gaya miki za ki daure ki yi amfani da ita?" Hafsat ta ce" eh insha'Allah" Safiyya ta ce "ni a gani na ki hak'ura da Abeed zai fi, don alamu sun nuna ba ya son ki, kuma baya muradin zaman aure da ke, to hak'ura da shi zai fi alkhairi, don gaba na ke jiye miki, ki manta da duk wani buri da ki ka Sakawa zuciyarki akan auren Abeed, ki yi watsi da maganar, ki nemi za6in Allah kawai". Jinjina na kai kawai Hafsat ke yi, alamum maganar ta shigeta, ta ce "dama nima zuciya ta, tana ta mun waswasi akan maganar, amma tun da yanzu kin haska mun inda na kasa ga ni, insha'Allah na janye daga yau, dama umman mu tana ta tambayata akan maganar tana son ji yadda mu ka yi da Abeed, ina ta mata hanya_hanya, tunda abun ya kasance haka zan sanarda da ita na fasa kawai, ta sanar da Abbanmu, tunda dama ba dole aka mun ba, za6i aka ba ni". Safiyya ta ce "gaskiya kam, Allah ya sa hakan ya zama alkhairi," ameen k'awar kirki Hafsat ta fad'a tare da mika mata hannu suka tafa su na dariya. ***** Yau Daddy tunda ya dawo ya ke zabga fad'a, mummy ce ta sauko tana fad'in Alhaji lafiya? tun daga sama na ke jiyo maganar ka, mai ya faru ne? Daddy ya ce "ni da yaron nan ne Muhammad, d'azu Alhaji Usman ya ke gaya mun, wai yarinyar wajensa ta janye maganar aure tsakaninta da shi, kuma na san ba komai ya saka ta yi hakan ba, sai dan bak'in hali da ya ke nuna mata, tunda tun fil'azal ya nuna baya son aurenta kawai dai tilasta shi mu ka yi". Mummy ta ce "yi hak'uri Alhaji, bari ya zo, na tambaye shi yanda suka yi da yarinyar," Cikin 6acin rai Daddy ya ce "ba na son Jin komai daga gare shi, kawai idan ya dawo ki sanar da shi cewa na yanke hukuncin ba zai kuma yin wani azumi a gidannan ba, sai a gidan aurensa, don haka ya shirya kafin azumin nan mai zuwa za a yi aurensa , gobe_goben nan zan sanar da shi yarinyar da zan kuma nema masa, don haka ya yi gaggawar zuwa su shirya kansu". Daga haka bai kuma cewa komai ba, ya wuce fuuuu ya haye sama, Mummy kam tsayawa ta yi baki bud'e, don tasan mutumin na ta, idan ya ce eh, baya ta6a dawowa ya ce a'a...... Mujee zuwa Auntie M Jabo 🍃 & Maman Twins 😍 : 💫AN YI WALK'IYA 19&20💫 ©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo ®NWA Abeed na dawowa, Mummy ta same shi domin isar da sak'on Daddy, nan take ta zayyana masa hukuncin da Daddy ya yanke akan maganar aurensa, zare dara_daran idanunsa waje ya yi, tare da fad'in "Mummy kafin azumi fa kika ce ni duk kun bi kun saka min ido ga mata nan ba'a tsangamesu ba saini, tsakani da Allah azumin da bai fi 3 months ba, how comes zan iya aure kafin lokacin, bayan na san ko yanzu wadda Daddy zai nema mun ba lallai ta dace da ra'ayina ba," Jinjina kai Mummy ta yi tare da fad'in "Abeed har yanzu ba ka hak'ura da wannan mummunan k'udirin naka ba ko?, nidai kan gani nake Ka yi hakuri ka kar6i za6in mahaifinka ya fiye ma ka." Abeed ya ce "Mum ba wai na k'i bin maganar Daddy ba ne, Noo, ki gane mana, nima fa ya kamata a duba uzurina a yi mun adalci, don ni ba k'aramin yaro ba ne, da za a ce bani da hankalin da zan za6i matar da ta dace da ni, kuma ni ba mace ba bare a mun auren dole," ya had'e hannayensa wuri d'aya, ya cigaba da fad'in "please mum ki taimaka ki gayawa Daddy ya hak'ura da zancen auren nan yanzu, har sai na samu irin macen da na ke son aura". Ajiyar zuciya mummy ta sauke, sannan ta ce "Abeed ka san halin Alhaji sarai, tun da ya taso da maganar nan, Allah kadai zai hana a yi aurenka a tsukun lokacin da ya fad'a , ni dai shawarar da zan ba ka, ka daure ka amince da abun da mahaifinka ya fad'a". Ba don ransa ya so ba, ya ce "to" saboda ya fuskanci ita ma mummy ta kasa fuskantar in da ya sa gaba. K'ofa mummy ta nufa tana fad'in "Ni dai sai da safe, don har na fara Jin barci," Abeed ya ce. "Allah ya tashe mu lafiya". Tunda safe Daddy ya sa aka kira masa Abeed, nan da nan kuwa ya hau kora masa bayani akan yarinyar da ya kuma nema masa don sun riga sun gama magana da mahaifin ta, ya ce "Muhammad ai kasan Alhaji sulaiman ko"? Gyd'a kai Abeed ya yi don kaf abokan Daddy ba wanda bai sa ni ba, Daddy ya cigaba da cewa "To ya baka babbar 'yar sa, sai ka je ku daidaita kan ku, shiru Abeed ya yi na dan lokaci, sannan ya ce " to tare da mik'ewa ya na fad'in "Bari na je na yi shirin zuwa office kada na makara". Daddy ya ce "ya yi kyau, Allah ya taimaka", Abeed ya ce "Ameen" tare da fitowa. Bayan ya dawo daga office, wannan karon bai jira Mummy ta yi masa maganar zuwa ganin yarinyar da aka kuma ba shi ba, ya shiga shirin zuwa, nan da nan ya fesa wankan shi, ya d'auko wata dakakkiyar shadda grey colour ya saka, ya murza hularsa kalar shaddar, ya sha perfumes masu sanyin k'amshi, ya fito fes da shi, a parlor su ka had'u da mummy ta kalleshi ta ce "sai ina kuma"? Murmushi ya yi wanda bai kai ciki ba, ya ce "Mummy wurin yarinyar da kuka ba ni mana" murmushin Jin dad'i mummy ta yi, ta ce "yawwa my boy, haka na ke so, Allah ya kiyaye hanya, Allah kuma ya dawo mun da kai lafiya," ya ce "Ameen Mum," tare da ficewa daga parlourn. Driving ya ke yi, yana sauraren wani cool music, amma duk da haka zuciyarsa ba ta daina masa tuk'uk'in da ta ke yi ba, don dai ya fito zancen nan ne don ya cimma burin da ke zucuyarsa, lokaci d'aya kuma sai ya saki wani murmushin Jin dadi don tuna abinda ya k'udire a zuciyarsa, hakan ya yi dai_dai da k'arasowarsa gidan Alhaji Sulaiman... Auntie M Jabo🍃 & Maman Twins 😍 💫AN YI WALK'IYA 💫 ©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo ®NWA Horn ya yi mai gadi ya wangale masa gate ya shige, wannan karon direct parlourn gidan ya nufa, bayan ya shiga sun gaisa da mutan gidan, aka ce ya zauna a turo masa yarinyar mai amsa sunan Teema, gaishe shi ta yi cikin kunya da ladabi, ba laifi shima ya d'an saki fuskarsa, don ya ga alamun zata yi hankali, amma duk da haka natacciyar zuciyarsa na masa hud'ubar tsiya, don haka nan da nan ya fuske, ya hau zayyana mata sharuddansa,ita ma ba ta tsaya wani dogon nazari ba tace da shi dama tana da wanda take so, don dai babanta ya zo da maganarsa ne shi yasa ta amince, amma tunda abun haka ne idan don ita ne ta janye akai kasuwa, murmushin cin nasara Abeed ya yi, don dai ya lura ba za a samu matsala ba a wurin teema ba, don haka cikin wayo da dabara irin na d'a namiji ya nuna mata, ta sanarda daddynta ya yi hakuri ya janye maganar auren su, tunda tana da wanda ta ke so, teema ta ce "Ba damuwa idan dai Daddy na ne bai da matsala zai fahimce ni". Murmushi Abeed ya yi tare da mik'ewa ya ce "To ni zan ta fi" teema daga nan zaune ta ce "Allah ya kiyaye hanya". Ya ce "Ameen" tare da fitowa daga parlorn, cikin nishadi ya ke driving d'in sa har ya zo gida. A parlor ya tarar da Mummy a zaune, tana kallon T.V, ta ce "welcome back, yarona har ka dawo ke nan"? Ya ce "Eh mummy ba ki yi barci ba ne "? Tace "Eh ina nan, ina jiran dawowarka ne, amma daga ganin alamun fuskar nan ta ka an dace," dariya ya to tare da fad'in "i hope so", Mummy ta ce "Allah ya sa" yace "Ameen " tare da fad'in "Mummy bari na je na kwanta, wallahi duk a gajiye na ke". Mummy ta ce "Ai ko ni tashi zan yi, don su Arfat tun d'azu suka yi barci, nima don na tsaya jiranka ne. " Yau ta kama asabar daga Daddy har Abeed ba wanda ya je aiki, suna hutawa a gida, don haka sai can wajen yamma Alhaji Sulaiman ya yi tattaki zuwa gidan don sanarda da Daddy halin da ake ciki game da auren Abeed da teema, tunda ya gaya masa baya son a dauki wani dogon lokaci kafin a yi auren. Bayan sun gama tattaunawarsu a cikin gidan, suka fito Alhaji Sulaiman ya na cewa "Alhaji Bashir hakuri za ka yi, kasan komai nufin Allah ne, Allah bai kaddari matarsa ba ce, kasan yaran yanzu ba a musu dole, wata k'ila matarsa tana can wani wuri inda ba a zata ba". Gyada kai Daddy kawai ya yi, amma a k'asan zuciyarsa yana tunanin, taurin kai irin na Abeed, da haka suka yi sallama da Alhaji sulaiman, Daddy yana shiga gida ya rufe Abeed da fad'a ta inda yake shiga bata nan yake fita ba, daga karshe ya kuma tabbatar masa da aurensa yana nan ba fashi kamar yadda ya fad'a sai dai duk abinda zai yi ya je ya yi............. Maman Twins 😍 & Auntie M Jabo 🍃 [4/11, 2:55 PM] 💫AN YI WALK'IYA 29_30💫 ©Mrs Saif & Hauwa M Jabo ®NWA Abeed ne ya fara rarrashinta, yana cewa ki yi hak'uri Afrat , komai muk'addari ne duk abinda kika ga ya faru da bawa to haka Allah ya tsara masa." Da haka ya yi ta tausar Afrat da kalamai masu sanyaya zuciya har suka iso gida. Washe gari ta kama ranar laraba, a ranar aka sallame su arfat daga asibiti, don ta warke sumul sai dan abinda ba'a rasa ba. Tunda suka dawo gida Arfat ba ta wata doguwar magana bare hira daga eh sai a'a, hakan da take yi ba k'aramin tadawa mutanen gidan hankali yayi ba, musamman mummy da Afrat. Mummy ce ta shiga d'akin su Arfat don yin magana da ita, kamar dai yadda ta koma tun faruwar al'amarin haka ma yanzu mummy ta tarar da ita a zaune ta na aikin tunanin da ta saba. Zama mummy ta yi akan gadon da Arfat ke zaune, sannan ta janyo ta jikinta, cikin sigar rarrashi ta fara magana "haba Arfat yanzu rayuwa ta yiyu a haka??? Duk Kin bi kin chanza, kin daina walwala,, ba kya son cin abinci, kullum ba ki da aikin da ya wuce zama a d'aki kina tunani, haba Arfan mummy why "?? Ta k'arashe maganar tare da shafa kanta. Hawayen da take ta mak'alewa ne suka samu damar gangarowa a kumatunta ta ce "Mummy kun k'i ku gaya mana asalin mu, kullum idan na yi magana sai ku ce za ku fad'a, amma har yau shiru ga shi kwanaki sai dad'a ja suke yi ". Ajiyar zuciya mummy ta sauke, sannan ta ce " abinda ya sa ba a gaya muku ba Arfat, ba ma so ne ki kuma shiga halin da kika shiga a baya, shi ne kawai ". Still hawayen ta ke yi ta ce "mum hakan da kuka yi, shi ya ke barazanar jefani wani hali, domin mummy yanzu buri na bai wuce nasan ni wacece ba, daga wani tsatso muka fito ni da k'anwata, ba ni da wani muradi da ya wuce hakan, domin Jin ainihin labarin mu shi zai kwantar mun da hankalina". Mummy ta ce "Arfat kin yi alk'awari, idan aka gaya miki za ki kwanta da hankalinki?? Za kuma ki dawo da walwalarki, ki dawo dai Arfat da na sa ni da bata yanzu ba, kuma ki kar6i labarin hannu bibiyu a duk yanda ya zo miki, kin yi alk'awari??? Arfat ta ce "yes mum, i promise you" Dad'a rungumeta mummy ta yi, ta ce "yawwa my lady, haka na ke son ji". Sannan mummy ta cigaba da fad'in "to ki kwantar da hankalinki idan Allah ya yarda Alhaji na dawowa za'a sanarda ku komai". Murmushi Arfat ta yi, for the first time, tun faruwar lamarin, ta ce "to mummy na gode". Murmushin mummy ta maida mata tare da mik'ewa tsaye ta mik'a wa Arafat hannu alamar ta mik'o na ta hannun su fito tare a dole Arfat ta mik'e suka fito daga d'akin, mummy na rik'e da hannunta har suka fito parlour. Arfat suka tarar a zaune tana kallo, duk da dai ita ma idonta ne kawai akan TV amma zuciyarta ta tafi bulayi, shigowarshi ne ya dawo da ita duniyar da ta shiga, da murnar ta mik'e tana fad'in "ah! Sisto yau an fito kenan??? Mummy ta ce "hmmm! Ga ta nan na 6a66akota dak'yar " Mummy ta k'arashe maganar da yin Murmushi. Afrat ta ce " Mummy aikam kin kyauta, don yawan zaman d'akin ita kadai yana k'ara mata damuwa." Mummy ta ce "sosai kuwa, bari na je na k'arasa girkin can, don yamma sai dad'a gabatowa take yi, tun da dai ku kun yi wa kitchen yaji kwana biyu". Murmushi suka yi dukan su, tare da cewa "Mummy za mu dawo ne very soon". Mummy ta ce "Allah yasa tare da shigewa kitchen. Auntie M Jabo 🍃 & Mum Twins 😍 [4/11, 2:55 PM] 💫AN YI WALK'IYA 26-28 💫 ©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo ®NWA Daga nan Abeed bai zarce da Arfat ko'ina ba sai asibitin Dr. Usmam wato family doctor d'in su. Asibitin mai amsa sunan Apex Clinic da ke nan cikin nasarawa G.R.A, tun kafin ya k'arasa asibitin ya kira Dr. Usman ya sanar da shi halin da ake ciki. Don haka suna isa doctors suka rufu akan ta, cikin taimakon Allah ba'a d'auki wani dogon lokaci ba ta farfad'o. Mummy kuwa bayan fitar Abeed d'auke da Arfat , side d'in ta ta nufa da niyyar d'auko mayafi don ta bisu, sai da bayan ta fito waje sai ta ga wayam,ba Abeed ba motarsa, hakan ya tabbatar mata da sun tafi asibiti ne. Juyawa ta yi gurin da Afrat dake tsaye ta yi wani zuru-zuru da ita, cikin rashin k'arfin jiki tace "Afrat yi sauri d'auko mun key d'in motata mu tafi". Afrat tace, "To" Tare da komawa cikin gida. A k'ofar shiga parlour suka had'u da Daddy shima yana shirin fitowa don zuwa asibitin. Yace "Ya dai Afrat, ba ku tafi ba ne"?? Afrat ta ce "Eh Daddy, yanzu za mu tafi, na shiga ciki ne, key d'in motar Mummy zan d'auko". Daddy ya ce "Waye zai yi driving d'in?? Afrat ta ce "Mummy ce" Daddy ya ce "Bar key d'in mu je a tawa motar kawai". Waje suka fito in da Mummy ke tsaye, Daddy ya ce "Maryam ta yaya za ki yi driving a irin wannan halin?? Sanin kan ki ne ban fiye son kina driving ba, bare ki na cikin wannan yanayin, abinda za a yi ku zo mu je manu driver ya kai mu gaba d'aya hakan zai fi". Mummy ta ce "Shi kenan dama na k'agara na ga halin da take ciki ne shi yasa". Murmushi Daddy ya yi, ya ce "Mummyn yara kenan yanzu za ki ganta Insha'Allah". Bayan sun isa asibitin a reception su ka tarar da Abeed, da sauri Mummy ta k'arasa in da Abeed ke zaune ta ce "Abeed ya jikin nata, Allah dai ya sa ta farfad'o "??? Abeed ya ce "Mum ki kwantar da hankalinki, Arfat ta farfad'o tun dazu, don dai an mata allurar barci ne, da ido biyu za ku tarar da ita". Gaba d'ayan su suka yi murmushi tare da fad'in "Alhamdulillah" Dai_dai lokacin Dr usman ya k'araso wurin yana fad'in, "ah! Alhaji har kun k'araso ke nan"?? Daddy ya ce "Eh Dr. ya aiki "?? Dr usman ya ce " Alhamdulillah!" Anan dai duk suka gaisa cikin girmamawa, sannan ya ce "Ai za ku iya shiga ku dubata" Daddy ya ce "ok." Dr. na gaba suna biye har d'akin da aka kwantar da Arfat, Mummy da hanzarinta ta k'arasa wurin gadon da Arfat ke kwance, ta ce " sannu Arfat " Abeed shima K'arasawa ya yi wurin, ya ce "Mum ke nan, barci fa ta ke yi, ki ke ta faman yi mata sannu". Murmushi kawai Mummy ta yi, ta cigaba da kallon Arfat, fuskarta ta yi fayau, har ta d'an fad'a, ta kuma k'ara haske, sai gashin kan ta da barbazu ko'ina har ya kusan rufe kyakyawar fuskarta. Hannu mummy ta saka ta na tattaro gashin har ta hade shi gaba d'aya ya yi baya, sai dai ba ribbon d'in d'aurewa. Kamar Afrat ta San tunanin da Mummy ta ke yi, ta ce "Mummy bari na ciro ribbon d'in kaina sai ki d'aure mata da shi". Mummy ta ce "Yauwa Afrat da kin kyauta kuwa". Daddy ne ya kalli Mummy ta gefen ido ya yi murmushi domin har ga Allah ya na k'aunar matarsa, ko don kyawawan halayenta, domin mace ce d'aya tak, amma tamkar da d'ubu. Likitan ne ya yi magana ya ce. "Ai matsalar ta ta, ba wata babba ba ce, dan stroke ne ta samu sakamakon razana da ta yi, sai dai don Allah hajiya a rik'a kiyaye abinda zai saka ta damuwa don gudun kuma faruwar haka". Mummy ta ce "Insha'Allah Dr. Yanzu zuwa yaushe za a sallame ta"?? Dr ya ce "ko gobe ma za a iya sallamar ta" Mummy ta ce "Allah ya kai mu" Suka amsa da ameen. Daddy ya ce "Yanzu ya za a yi, za ku koma gida ne ku shirya ko kuwa?? Don na ga ba ku d'auko ko mai ba". Mummy ta ce "Gaskiya ni Alhaji ina nan, sai dai ko ku je da afrat, ta dawo tare da jummai ko da abinda za ta yi mana anan". Kwa6e fuska Afrat ta yi, kamar za ta yi kuka ta ce ta ce "Mummy nima gaskiya ina tare da ku" Murmushi Daddy ya yi, ya ce "Mummyn yara ke nan to kin ji abinda 'yar ta ki ta ce ita ma,saboda haka duk ku taso mu tafi gaba d'aya kwa dawo daga baya, tunda kun ji Likita ya ce sai zuwa 8pm ko zata tashi, kun ga kuma kwa shirya a tsanake, tun da akwai nurses masu kula da patients". Mummy ba a son ranta ba ta tashi sai don kar ta yiwa Daddy musu. Gaba d'ayan su suka fito da niyyar komawa gida, har Abeed don dai shima a gajiye ya ke lik'is don tun farkon faruwar al'amarin baya samun cikakken barci, don gudun abinda zai je ya dawo. Abeed ne ya fara shiga motarsa shi da afrat suka tafi, sannan Daddy suka shiga ta su, shi da Mummy manu driver ya ja suka tafi. Bayan sun fara tafiya ne, Afrat ta juyo da dubanta zuwa ga Abeed ta ce "Ni kam bros abinda ya faru yana ba ni mamaki ba kadan ba, wai ta yaya mummy za su ce ba su, suka haifemu ba, bayan dai dai da minti d'aya ban ta6a ganin sun nuna wani abu da zai nuna ba su suka haifemu ba." Abeed ya ce "Ba ke kadai ke mamaki ba Afrat, ni kai na abin ya yi masifar d'aure mun kai, a ce dukan ku, ku biyu ba su suka haife ku ba, duk da cewa, duk wanda ya kalleku ya san ciki d'aya kuka fito don tsananin kamar ku." Afrat ta ce " wallahi bros babban burina yanzu bai wuce na san su waye suka haife mu ba, kuma na san ta yadda mu ka zo hannun su mummy.... " Sai kuma wasu hawaye suka fara saraftu a fuskarta....... Auntie M Jabo 🍃 & Mum Twin💫AN YI WALK'IYA 31_32💫 ©Mrs Saif & Hauwa M Jabo ®NWA K'arfe takwas na dare, gaba d'ayan su sun hallara parlourn Daddy, kamar yadda aka saba Daddy ne ya fara magana kamar haka "mummyn ku ta sanar da ni duk abinda ku ke ciki musamman ma Arfat akan maganar da aka fara kwanakin baya ba a k'arasheta ba, sakamakon wasu dalilai, amma bayanin da ta zo mun da shi yanzu ya nuna bayyana muku ainihin maganar shi zai samar muku da kwanciyar hankali a zuciyarku don haka muka yanke shawarar sanar da ku ainihin labarin iyayenku." A iya sanin mu iyayenku mutanen kirki ne, domin duk tsawon shekarun da muka shafe tare ba mu ga wani mummunan hali a tare da su ba, asalima ba 'yan nan k'asar ba ne,yan k'asar nijar ne,Allah ne ya hada mu da su kusan shekaru ashirin da biyu da suka wuce. A wancan lokacin ba a wannan unguwar muke ba, muna wata unguwa da ake kira tarauni, anan dai cikin birnin kano, wata rana muna zaune ni da mummyn ku da dare bayan sallar magrib, wani yaro ya shigo ya ce "wai Ana sallama da ni a waje". Na ce "da shi ya ce ganin zuwa, bai dade da fita kuwa nima na fita. Sai dai wad'anda na tarar a tsaye a wajen, abin ya matuk'ar ba ni mamaki, don ban San fuskokinsu ba, a haka dai na tsaya muka gaisa, namijin ne ya fara magana cikin hausar sa wadda ba ta fita sosai, don kana ganin su ka san buzaye ne, "Alhaji alfarma muka zo nema a gurinka" Na ce "Allah yasa zan iya" Ya ce "suna so ne idan da hali su zauna tare da mu, shi zai riqa yi mana gadi, matarsa kuma zata rik'a taya hajiya aiki" Na d'an yi Jim! Na d'an lokaci, sannan na ce "gaskiya ni ba ni da sha'awar mai gadi, domin a wancan lokacin arzik'i na bai kai haka ba, ina da kudi daidai gwargwado, don kusan layin da muke ba wanda ya kama k'afar arzik'i na. Anan dai suka hau yi mun magiya, har matar da suke tare ta matso wurin da nake tsaye, ta durk'usa ta ce "don Allah Alhaji ka taimaka mana, don idan muka bar nan ba musan in da zamu dosa ba, duk inda muka je gudun mu ake yi, wani wuri har jifan mu aka yi, aka mana korar kare", ta k'arashe maganar da sakin kuka mai ban tausayi. Har cikin raina na tausaya musu, sai dai tunanin yadda duniya ta lalace, nake yi ka yi wa mutum alkhairi ya saka Maka da sharri, tun a wancan lokacin ma, bare yanzu da komai ya k'ara ta6ar6arewa. Duk da wasu ke 6ata wasu, ba duka aka taru aka zama d'aya ba. Saboda haka na ce da su "yanzu ka ga ni ban San ku ba, ban san abinda ya fito da ku daga gida, ka ga kuwa haka kuram bana d'auke ku na kai gidana ba". Ya ce "Alhaji wallahi mu ba mugaye ba ne, k'addara ce kawai ta fito da mu daga gida , sakamakon wani iftila'i da ya faru... Mu 'yan kasar nijar ne, nijar d'in ma wani k'ungurimin daji, a nan cikin dajin k'auyen mu yake, mai suna Salmau , mutanen k'auyen gaba d'aya ba mu wuce 200 ba, kuma kusan dukanin mu dangin juna ne, muka taru muka tada k'auye guda, don ko aure a tsakanin mu ake hadawa. Wata rana da daddare muna kwance wata iska mai k'arfi ta taso, kanka ce me, ta fara tuge mana 'yan bukokin mu,anan fa hankalin mu ya tashi, nan da nan aka tsuge da wani irin ruwa mai tsananin k'arfi, a hankali ruwan ya fara tafiya da mutane, kan wani lokaci kusan rabin duk ruwa ya tafi da su, wasu kuma ruwan na Jan su,, suna ihu, ba muda abinda za mu iya musu, haka muka hak'ura muka kyalesu, don muma Allah ne ya yi da shan ruwan mu a gaba. Ko da gari ya waye, wadanda suka tsira ba mu da yawa, kusan duk an mutu, wasu ma ba a ga gawawwakinsu ba, ciki kuwa, har da iyayen mu da sauran 'yan uwan mu na jiki. To tun daga faruwar al'amarin muka yanke shawarar barin garin, ni da mai d'akina, amma mun sha bak'ar wahala kafin mu zo nan Alhaji. Daddy ya juya ya kalli Arfat da Arfat da tunda aka fara ba su labarin idon su ke zubar da hawaye ya ce "a gaskiya a yanda mahaifinku ya sanarda ni, ba k'aramar wahala suka sha kafin su k'araso k'asan nan ba, don ya ce tun daga k'auyen su har zuwa garin marad'i a k'afa zuka je, kasancewar a wancan lokacin ba hanyar abin hawa da zata kai mutum cikin gari, sai keken shanu, shi kuma duk masu irin aikin haddasu iftila'in ya shafa. Sai da suka shafe kusan wata uku da kwanaki suna tafiya kafin su isa, ga shi ba su da wani wadataccen guzuri, suka yi ta fama da matsananciyar yunwa, wani lokacin har da k'ishi...... Auntie M Jabo 🍃 & Mum Twins 😍 [ 💫AN YI WALK'IYA 23-25💫 ©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo ®NWA Mummy na tashi daga nan straight 6angaren Daddy ta nufa, a zaune ta same shi, ita ma neman kujera ta yi ta zauna jikin ta duk a mace, sannan ta ce "Alhaji yaran can fa suna can duk sun d'aga hankalinsu akan maganar da suka ji, ya kamata a musu bayani ko hankalinsu zai kwanta." Daddy ya ce "haka ne, dama ai dole a yi musu bayani, 6acin da raina yayi ne na taho ba tare da na musu bayanin komai ba." Mummy ta ce "hakuri za ka yi Alhaji ka san sha'anin yaro", Daddy ya ce "Ai shi ke nan, ya wuce, yanzu kin ga lokacin sallah ya gabato, bari na je masallaci, kafin na dawo kuma kun yi sallah, sai mu kuma wani zaman". Mummy ta ce "hakan za a yi, bari nima na tashi". Bayan an idar da sallah, Daddy da Abeed tare suka dawo daga masallaci, da ganin fuskar Abeed kasan yana cikin rud'u, Mummy kuwa ita da su Arfat tuni suma sun idar da ta su sallar, zaman jiran dawowar Daddy Kawai su ke yi, sai da suka nemi waje suka zauna, sannan Daddy ya fara magana. "D'azu na gaya muku mun yanke shawarar had'a auren kai Muhammad tare da 'yar uwarka Arfat! Ba don komai muka yi hakan ba, sai don sanin akwai aure tsakaninku, tsaftatacce ma kuwa, wanda Allah (S W A) ya halatta muku". Tuni fuskar Abeed ta sark'e da ta Arfat, suna kallon junansu, dukaninsu mun hango tsabagen mamaki a idanuwansu, Daddy ne ya katse musu tunani ta hanyar cigaba da magana "domin kuwa a cikin ku akwai wanda ba mu muka haifa ba...!!! Gabansu ne ya tsananta fad'uwa, har afrat dake gefe tana matsar k'walla, da sauri Arfat ta fad'a jikin Mummy tana kuka take fad'in Mum don Allah mu dai kar ku ce ba ku kuka haifemu ba, don duk duniyar nan ba mu San kowa ba sai ku Mummy," k'arashe maganar tare da sakin wani irin kuka, rungumeta Mummy ta yi tsam, kamar za'a k'awata ta ce "Arfat dama kaf duniyar nan mune iyayenku kowa yasan haka, kada ma ki yi shakkar haka, wannan maganar an taso da ita ne kawai don a warware wata matsalar". Sai kuma ta juya wurin Daddy tana fad'in "Alhaji don Allah abar maganan haka, tunda dai an gaya musu akwai aure a tsakaninsu, kuma sanin kan su ne ba za mu had'a haramtaccen Abu ba don son zuciyar mu, shi yasa tun fil'azal ban so aka bayyana wannan sirrin ba, don ni a tunani na barin zai fi mana kwanciyar hankali". Murmushi Daddy ya yi, ya ce "Maryam ke nan gwanda da kika ce a tunaninki, amma maganar gaskiya barin wannan maganar ba shi ne mafita ba, domin yin hakan shi zai haddasa tashin tashina a tsakanin su yaran". Abeed da tun dazu bai ce komai ba, idan ban da wulla ido da yakeyi, dak'yar ya kalato wani yawu ya had'iye a bushashshen mak'ogwaronsa, sannan ya ce "Mummy gaskiyar Daddy, don mu kanmu idan aka fayyace komai sai mun fi samun kwanciyar hankali". Jinjina kai mummy ta yi, tare da d'ago da kan Arfat dake kwance a cinyarta ta ce "Arfat kin ji abinda d'an uwanki ya fad'a kin amince a bayyana komai"??? Da k'yar Arfat ta iya d'aga kanta ta nuna alamar eh, don ita kadai ta san halin da take ciki. Daddy ne ya cigaba da fad'in " Gaskiyar magana Arfat da ke da afrat ba mu, muka haife ku ba.!!!" Dam! dam!! K'irjin Arfat ya dinga bugawa, sai kuma ta ji parlourn gaba d'aya yana juya mata, cikin k'araji ta ce "Mum kin ji abinda Daddy ke fad'a ko"?? Wai ba ku ka haife........ Sai kuma ta yi dif sakamakon duhun da taga ya mamaye mata idanuwa,, nan da nan ta yi baya da niyyar faduwa. Da sauri Abeed ya rik'ota ta fad'a jikinsa, sai dai gaba d'aya babu alamar numfashi tare da ita. Afrat da gudu ta yi kanta tana fad'in "sis Arfat don Allah kar ki mutu ki bar ni! Mummy don Allah ku gaya mata ku ne kuka haife mu, ta tashi". Sai kuma ta fashe da wani irin kuka mai ban tausayi, ita kanta mummy kuka take yi sosai, cikin kukan ta ce "Alhaji ka ga abinda na guda ko?? Domin nasan halin Arfat da saka abu a rai, yanzu wannan maganar zata iya janyo mata wani ciwon". Daddy ya ce "yanzu ba lokacin tsayawa yin wannan maganar, a yi kokarin ceto rayuwar ta tukun". Sai ya kalli Abeed ya ce "Muhammad dubo numbern Dr. Usman, ka kira ka ce ya zo yanzu ina neman sa". Abeed ya ce "Dad ai da d'aukan ta a ka yi kawai aka wuce da ita asibiti kaitsaye da zai fi, ko da asibitin Dr. Usman d'in ne, tunda kusa ne, ba nisa sosai." Daddy ya ce shike nan hakan za a yi, nan da nan Abeed ya suri Arfat, bai ajiye ta ko'ina ba sai bayan motarsa, bai jira fitowar su Mummy ba, ya ja sai asibiti....... Www.hauwajabo.blogspot.com Www.jabohauwa.WordPress.com Auntie M Jabo 🍃 & Mum Twins 😍 [4/11, 8:36 PM] Eve Jabo: 💫AN YI WALK'IYA 💫 33 & 34 ©Mrs Saif & Hauwa M Jabo ®NWA Haka suka yi ta fad'i tashi har suka iso garin Kano. To bayan ya gama ba ni labarin nima na shigo na sanarda Mummyn ku, da yake akwai ta da tausayi nan da nan ta amince, mu ka yanke shawarar mahaifinku zai rik'a yi mana gadi, ita kuma ummanku idan Allah ya sauke ta lafiya za ta rik'a taya Mummyn ku aika_aikacen gida, da yake ko da suka zo tana d'auke da tsohon cikin ki, ya nuna Arfat da hannu. Ba su dade da zuwa ba kuwa, aka haifeki, yarinya mai kyau da ke, ga farin jini, kusan ko da yaushe a wurin Mummyn ku kike wuni, kasancewar ta mai son yara, don haka ba k'aramin sabo ku ka yi ba. Ba ki fi 2 years ba ta haifi Afrat , don haka Arfat sai ta koma hannun Mummy da zama gaba d'aya. A kwana a tashi ba wuya, ita ma afrat ta fara girma sai ta nuna, ta fison zama gurin Mummyn ku akan gurin ummanku, don wata rana da kuka take tafiya idan ta zo d'aukanta, Mummyn ku ta ce ita ma a kyaleta a wurin ta tunda ta fison nan, ummanku sai dai ta yi murmushi kawai, don akwaita da kawaici, kuma tana Jin dad'in yadda Mummyn ku, ke nuna k'aunarta a gare ku. Haka rayuwan mu ta cigaba da kasancewa har zuwa ranar, wata juma'a da ba za mu manta da ita ba, muna kwance misalin k'arfe biyun dare, wani irin k'auri ya tashe mu, a firgice muka fito harabar gidan, ai kuwa nan da nan muka hango wani irin hayak'i yana tashi daga boys quarters , ba shiri muka nufi can, ashe wuta ce ta kama, wadda ba mu san musabbabinta ba har yau, domin ko da muka je mahaifanku babu mai sauran numfashi, domin 90% na jikin su duk ya k'one." Hawaye ne kawai ke zubowa daga fuskar su Arfat tare da maimaita Innalillahi Wa'inna'ilaihirraji'un! Daddy ya cigaba da fad'in "duk abin nan da ke faruwa Abeed baya nan, yana k'asar Cyprus don tun yana da 4 years k'anina ya dage yana so a ba shi Abeed d'in don ya fara makaranta acan, don akwai makarantar da yaransa ke yi, da yake shi ya riga ni fara tara iyali, don wasu daga cikin yaransa duk sun girmi Abeed. Bai dawo Nigeria ba, sai da ya gama secondry school, sai dai mu muna ziyararsa time to time, kuma tun a wancan lokacin dama an gaya masa yayi k'anne don har pictures d'in ku ana tura masa. So that da ya dawo, ya tafi a zuwan ku kannensa ne uwa d'aya uba d'aya, don ko dangina na yi musu kashedin kar wanda ya sanar da ku, har sai lokacin da muka yanke, don ko da wannan maganar ba ta taso ba, mun yanke shawarar gaya muku, idan dai wa'adin da muka saka ya cika,sai ga shi kuma haka ta faru. Wanna shine abinda muka sani game da iyayenku". Arfat tashi ta yi daga in da take zaune, zuwa gurin da Mummy da Daddy ke zaune ta fara magana cikin kuka ta ce "Mum, Daddy ba mu da bakin da za mu gode muku, sai abinda na sani bakunan mu baza su ta6a daina muku addu'ar alkhairi ba, har sai ranar da numfashinmu ya bar jikin mu, haka iyayenmu daga yau za mu saka su cikin addu'a har ranar da Allah zai kar6i rayuwar mu, don addu'ar mu garesu shi zai sa su yi alfahari da haihuwar mu". Na yi matuk'ar farin ciki da suka, zama iyayenmu, domin babbar fargabata bai wuce a ce ba mu da iyaye ba, sai ta saki wani murmushi wanda yayi dai_dai da gangarowar wasu hawaye masu sanyi a fuskarta ta ce "Alhamdulillah! Daddy ne ya kalli gefen da Abeed ke zaune ya ce "Muhammad ka ji labarin 'yan uwanka, hope za ka rik'eta da amana tunda dai ka ji marainiya ce ". Hmm! Kawai Abeed ya ce tare da mikewa tsaye yana fad'in " ni duk na gaji dad, bari na je na d'an kwanta, na huta". Bai jira abinda za su ce ba ya wuce abinsa. Dukansu zuba masa ido suka yi, suna karantar wani abu a tare da shi, sai dai ba su kai ga lalubo amsar ba ya wuce. Yana zuwa d'aki ya zube akan gadonsa, yana sauke wata naunanniyar ajiyar zuciya, ya d'aga kan shi sama yana kallon fan, nan da nan ya Lula duniyar tunani..... Mum Twins 😍& Auntie M Jabo 🍃 [4/12, 9:00 💫AN YI WALK'IYA 💫35_37 ©Mrs Saif & Hauwa M Jabo ®NWA Ya fi k'arfin 1hr a kwance, yana tunani sai dai ya kasa lalubo mafita, don haka ya mike tare da sakin tsaki, key d'in motarsa ya d'auka ya yi waje, daga nan bai zarce ko'ina ba sai gidan su mubarak. Ya taki sa'a kuwa ya same shi, mubarak ne ya fito da murnarsa sai dai yanayin da ya ga abokin nasa ne ya sa gwiwarsa ta yi sanyi, ya ce "mutimina ya dai??? Na gan ka wani iri, me ya faru ne?? Tsaki Abeed ya kuma ja, sannan ya ce "wallahi wata matsala ce, ta dabaibaye ni, na rasa ya zan 6ullowa al'amarin gaba d'aya kai na ya kulle shi yasa, ka ga na zo wurinka, ko akwai mafitar da za ka nema mun". Mubarak ya ce "ina jinka abokina, gaya mun abinda ya faru". Abeed ya ce "ai maganar ce, fad'arta ma abun kunya ne, a gurina don na yadda da kai ne shi yasa ma har na zo gurinka, amma abun mtsss....... Sai kuma ya yi shiru yana girgiza kai, Go on, mubarak ya fad'a, tare da nuna alamar k'aguwa ya ji zancen. Abeed ya ce "tunda na zo ai dole na gaya Maka, nan da nan ya juyewa mubarak duk abinda ya faru. Murmushi mubarak ya yi, tare da cewa "Abeed ai wannan had'in na ku, ya yi wallahi, mai abun kunya a nan?? Ni da farko da ka fara magana na d'auka wani mugun abun kunya ka...... Abeed ya katseshi sakamakon d'aga masa hannu da ya yi ya ce "ya isa haka, ban saka ka dogon surutu ba, ni dai kawai na zo ka ba ni shawarar yadda zan su6ucewa auren ne, ba tare da ran su Daddy ya 6aci ba". Mubarak ya ce "Abeed idan dai shawarar kwarai ka ke so, to kada ka yarda ka bijirewa auren Arfat, don aurenku ba k'aramin da cewa ya yi ba. Hannu Abeed ya d'aga masa a zafafe ya ce "ta ina muka dace??? Tana matsayin 'yar mai gadi,kuma' yar mai wanke_wanke da shara, ba dacewa sam a tsakanin mu". Galala mubarak ya yi, yana kallonsa, ya ce "Abeed ai wannan sirrin gidan ku ne, ba wanda zai san da haka, sai dai idan ku kuka fasa kowa ya ji." Abeed ya ce "ta yaya za a ji zan auri k'anwata, ka ce duniya ba ta tambayi ta yaya haka ya kasance ba, kuma sanin kan ka ne dole'yan matan da suka yi haukan so na, su yi mun dariya kuma ajina ya zube k'asa wanwar, idan an ji, zan aure 'yar maigadin gidanmu". Mubarak ya ce "gaskiya ka yi nisa ba ka Jin kira, amma ni ban ga aibun wannan auren ba". K'wafa Abeed ya yi, ya ce "yayi kyau", daga haka bai kuma cewa komai ba ya shuri takalminsa ya fice, mubarak yana ta k'wala masa kira bai saurareshi ba, ya yi gaba. Arfat kuwa tunda haka ta kasance, ta karbi za6in da aka musu hannu bibiyu, domin ta yi alk'awarin yi ma su mummy biyayya matuk'ar abinda suka sakata bai sa6awa shari'a ba, abu d'aya ta ke tunani ta yadda za ta kar6i Abeed a matsayin miji, bayan kallon da ta ke masa na d'an uwanta shak'ik'i, duk da dai ya hada duk wani abu da take buk'ata a d'a namiji, murmushi ta yi, sannan ta lumshe idonta, afrat da ke gefenta a zaune tana daddanna phone ta ce "sisto ke da waye ne?? Kike ta faman murmushi "? Zaro ido Arfat ta yi ta ce yaushe?? Don bata san ma ta yi ba,, nan da nan afrat ta d'ago ta, ta yi murmushi ta ce " share kawai " Kwanaki sai tafiya suke yi, amma har yanzu Abeed ya k'i tsayawa ya yi magana d'aya, duk lokacin da aka taso da zancen aurensu da Arfat sai yayi ta hanya_hanya. Har Daddy ya gaji yau ya titsiye shi akan sai ya gaya masa, mai ya ke nufi ne akan maganar aurensu. Daddy ne ke ce da Abeed "ba ka ji abinda na fad'a ba ne ka yi shiru?? Sosa k'eya Abeed ya hau yi, ya ce "Wallahi Daddy dama...... Sai kuma ya yi shiru, Daddy ya ce "dama me?? Ya cigaba da fad'in "wai da an ba ni dama na nemi wata, saboda gaskiya ni.... Sai kuma ya kuma yin shiru, a zafafe Daddy ya ce Ka cigaba da magana kar ka 6ata mana lokaci. Abeed ya cigaba da fad'in "gaskiya Daddy ba class d'ina ba ce saboda.... Ai bai ka ga K'arasawa ba Daddy ya d'auke shi da mari, sannan ya nuna shi da hannu ya ce "ban k'ara tabbatar da ba ka da tunani ba, sai yau, to wallahi idan kana son ka ga tsantsar 6acin raina ka bijirewa auren nan, don akan maganar nan zan iya sa6a Maka fiye da yanda ba ka zato". Daga haka bai kuma cewa komai ba, ya fice daga parlourn fuuuu! Mummy ma ta bi bayansa. Auntie M Jabo 🍃 & Maman Twins 💫AN YI WALK'IYA 💫38_40 ©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo ®NWA Jiki a sanyaye Arfat ita ma ta mik'e ta nufi dakin su, Afrat ta bi bayanta, tana rarrashinta, don ta hango damuwa a idon yayarta ta k'arara. Ya rage saura Abeed a wurin, yana tunanin me abin damuwa akan abinda ya fad'a, bayan gaskiyar abinda ke zuciyarsa ya fad'a, tabbas da a ce Arfat iyayenta ba su kasance mak'ask'anta ba, da ba abun da zai hana ya aureta, don tana da sifofin da yake so macen da zai aura ta kasance da su,da wannan tunanin ya bar wajen. 2 weeks later, tun daga ranar da Daddy ya tadawa Abeed maganar, bai kuma ce da shi k'ala ba har yau, ya zuba masa ido ne kawai yana jira ya ga ya saduda, ya bada kai bori ya hau. Ashe shi bai san Abeed yana can yana shirin tafiya ba, don har ya yi visa, ya siye ticket na tafiya k'asar Cyprus, gurin Baffa Abbakar. Sai tashi suka yi suka ga ba Abeed alamar sa, da farko sun za ci ya je office ne,sai aka yi ta kiran phone d'in sa is switched off, don haka Daddy ya kira office d'in su aka ce rabonsa da zuwa office, tun shekaran jiya, nan fa hankalin su mummy ya fara tashi. Wasa_wasa an doshi kwana uku ko labarin Abeed, ba su ji ba, duk wanda ke gidan hankalinsa ya kai k'oluluwar tashi, idan ka cire Daddy, don shi cewa ya yi duk inda ya je, shi ne mai dawowa da kansa. Washe gari sai ga Baffa Abbakar ya kira, yana shaidawa Daddy Abeed ya zo wurin su, kuma ya sanar da shi duk abinda ya faru. Ran Daddy ya yi matuk'ar 6aci don haka ya ce da Baffa Abbakar duk abinda ya ke yi ya ajiye ya taso k'eyar Abeed su dawo tare. Baffa Abbakar ba yanda ya iya,dole ya amince, don bai isa ya yiwa Daddy musu ba. Bayan ya gama wayar ne ya zayyanawa Mummy duk abinda ya faru. Ita ma ta yi mamakin abinda Abeed ya yi, sai dai yanda ta ga ran Daddy ya 6aci, ta danne na ta mamakin, ta hau ba shi hak'uri don ta san, in dai ransa ya 6aci irin haka komai yana iya faruwa. Yau ta kama asabar, wurin 2pm su Abeed suka iso, shi da Baffa Abbakar, sun samu kyakkyawar kulawa daga wurin mummy. Tun wurin la'asar gidan ya fara cika da 'yan uwan Daddy kai har da na Mummy, don duk wani d'an uwa na jiki ya zo, sakamakon gayyatar da Daddy ya musu na emergency meeting da za a yi after magrib. Sai wurin magrib Daddy ya dawo, bayan sun yi sallah gaba d'ayan su sun hallara, har Baffa Abbakar. Daddy ya fara magana. "Alhamdulillah! Ba abinda zan ce da Allah sai godiya, da ya nuna mun wannan ranar da na ke son sauke wani nauyi da ya rataya, a wuyana shekara da shekaru, hak'ik'anin gaskiya na ji dad'in kasancewar ku anan don ku zame mun shaida akan abinda zan fad'a, sanin kan ku ne abubuwa da dama sun faru a shekarun baya, kwanakin baya an warware wani sirri da ya dad'e a binne, haka ma yau ina tabbatar mu, da cewa, zan bud'e d'ayan sirrin, duk da dai ku, kun san komai, amma shi wanda abun ya faru akan sa bai sa ni ba. Sai ya juya 6angaren da Abeed ke zaune ya ce "Muhammad a yau ina bak'in cikin sanar da kai cewa ba mu muka haifeka ba, hasalima har maganan da na ke yi yanzu ba musan iyayenka ba....!!! Mum Twins 😍 & Auntie M Jabo 🍃 [4/16, 16)4:36 PM] MRS SAIF ✍🏻: 💫AN YI WALK'IYA 💫41_50 ©Mrs Saif & Hauwa M Jabo ®NWA Tashin hankali wanda hausawa suka ce "ba'a saka masa rana " don kuwa Tashin hankalin da muka hango cikin idanun Abeed ba zai ma misaltu ba, don dara_daran idanunsa sun k'ank'ance sun yi jajir kamar an zuba kwanon barkono a ciki,ya jik'e jagab da gummi duk da sanyin AC da ya game parlourn. Da kyar ya iya Jan jiki, ya je gurin da Daddy ke zaune, dafa k'afafuwan Daddy ya yi cikin k'uncin zuciya ya fara magana, daga ji ka san yana cikin tsananin rud'ani ya ce "Daddy don Allah ka yafe mun abun da na yi maka, kada ka hukunta ni ta haka, idan don auren Arfat ne Daddy wallahi ina son ta, kuma zan aureta, amma kar ku ce ba ku kuka haife ni ba". Murmushi Daddy ya yi sosai ya ce "yaro dai yaro ne amma, idan ban da abun ka Abeed haka kurum, zan k'irk'iri k'arya na fad'a, har na tara mutane irin haka, ko dai ka dimauce ne ba ka ga jama'ar da ke wurin nan ba??? To bari ka ji wannan maganar haka take duk wanda za ka tambaya haka zai gaya ma. Don ni da Maryam ba mu ta6a haihuwa ba, mun dad'e muna neman haihuwa, mun yi yawon asibiti gida da da waje amma Allah bai ba mu ba, duk in da muka je za a ce da mu, ni lafiya ta kalau, Maryam ce mai matsala, sai dai ko ita ana sa ran zata iya haihuwa nan gaba, a haka har muka share 10yrs da aure shiru, ita kuma ga ta da masifar son yara, ni kuma tsananin son da na ke mata ya saka ba zan iya had'ata da wata ba. Don haka muka yanke shawarar zuwa gidan marayu, mu d'auko yaro,don ya rik'a debe mana kewar yara.ko da muka je kuwa mun ci sa'a an kawo ka, wai an jefar da kai a bayan layi, to tunda muka d'ora idanmu akan ka Allah ya jarabe mu da tsananin k'aunarka musamman Mummyn ku, don kana jariri sosai a lokacin, bayan mun gama cike_ciken takardun da aka ba mu, daga nan asibiti muka wuce don duba lafiyarka, da kuma bawa maryam shawarwari ta hanyar da zata bi ta samu ingantaccen ruwan nono, don ta yi k'ememe ta ce ba za ta ba ka, madara ba, sa dai ta shayar da kai da kanta. Wannan shi ne takaitaccen labarinka, sai ya yiwa Mummy nuni da ta mik'awa Abeed takardar da ke hannunta, kar6ar takardar ya yi hannu na rawa, yana dubawa, takarda ce ta yarjejeniyar kar6ar yaro a gidan marayu, duk dauriya irin na Abeed, sai da ya zubar da hawaye, don takardar da ke hannunsa sai da ta jik'e jagab da hawaye. [4/16, 4:37 PM] MRS SAIF ✍🏻: Duk wanda ke parlourn sai da ya tausaya masa, ni kaina maman Twins na tausayawa Abeed matuk'a, juyawa na yi wurin da Jabo ke zaune, na ce "gaskiya Jabo Abeed ya ba ni tausayi ba kadan ba" Ta ce "gaskiya nima na tausaya masa, amma ai gwanda da aka yi WALK'IYA fuskar kowa ta fito ras. Na ce "haka ne kuma fa, kin ga AN YI WALK'IYA mun gano fuskar Abeed a zahirinta na gaskiya, ba wancan fuskar da mu ke gani a da ba". Mun shagala da surutu, ashe Daddy har ya cigaba da magana, sai tsinkayo muryarsa muka yi, yana cewa "don haka ke Arfat, kin ji asalin Abeed, idan kin amince sai a saka lokacin bikin ku nan ba da dad'ewa ba, Murmushi Arfat ta yi ta ce "Daddy kune iyayen mu duk abinda kuka zartar a gun mu dai-dai ne," Murmushi Daddy ya yi ya ce "Allah ya miki albarka, sannan ya juya gurin Abeed ya ce "na dawo gareka, duk da dazu ka ce ka amince, amma yanzu ina so na k'ara tabbatarwa shin ka amince kuwa??? Gyda kai Abeed ya yi tare da cewa "Daddy wallahi na amince" Daddy ya ce To, Alhamdulillah! Don haka na yanke shawarar d'aurin aurenku nan da 4wks, duk wanda ke parlourn sai da ya washe ba ki, ana fad'in Allah sanya alkhairi. Sannan Daddy ya ce "idan akwai mai son magana ya zo ya yi, an ba shi dama, kowa ya ce ba shi da magana, sai Mummy ta ce "ita akwai abinda za ta ce. Ta ce "ita Jan hankalinta akan yaran ne, don kar su ji an ce basu suka haifesu ba, tsiro da wasu halaye, ko kuma su rik'a jajjanye jikin su, na fiso ku cigaba da halanyanku kamar yadda muka saba, kada ku saka wani abu a ranku, mu ne iyayenku, kowa ya San da haka, don ko yanzu, ba kowa zai san halin da ake ciki ba, don mun yadda da danginmu, mutane ne masu rik'e sirri, da haka na ke mik'a godiya ta a gareku, Allah ya mai da kowa gida lafiya. Gaba d'aya aka amsa da ameen. [4/16, 4:41 PM] MRS SAIF ✍🏻: Kwanaki na tafiya biki na dad'a kusantowa, amma ango da amarya sai wasan 6uya ake yi, sukan su Mummy sai shirye_shiryen su ke yi, Abun ba kama hannun yaro. Can muka hango amarya Arfat, ta yi hanyar shiga d'akin angon na ta, da sauri muka bi bayanta don kar a yi ba mu. Akan gado ta same shi a kwance, ya yi rigingine, da sauri ya mike Jin muryarta, tana sallama, amsa sallamar ya yi, sannan ta nemi wuri ta zauna, ta ce "ya Abeed, sai da ya ji wani iri, a ransa don yadda lafazin sunansa ya fita a bakinta, don yanzu har ga Allah yana Jin son Arfat har cikin zuciyarsa, kawai kunyar abinda ya faru ne, ya saka ya kasa zuwa su fahimci juna. Itama Arfat ta fuskanci haka, shi yasa ta ajiye tata kunyar ta zo, sai da ta kuma maimaita sunansa sannan ya amsa. Ta ce "haba ya Abeed kullum mummy sai ta yi zancen mun k'i mu shirya kanmu ga biki sai kusantowa ya ke, that's why na zo yanzu, ko dai har yanzu ban yima ba, ta k'arashe maganar da sigar zolaya. Waro ido waje ya yi, ya ce ni na isa, kawai dai ina tuna abinda ya wuce ne , please Arfat for give me, I beg you". Arfat ta ce "come on, bros ka daina tuna abinda ya wuce, idan ka na tuna abinda ya wuce baza ka yi rayuwa mai dad'i ba, ni dama ban rike ka a raina ba. Murmushi Abeed yayi. Ya ce "thanks so much, my everlasting wife" Ita ma Arfat Murmushin ta yi, sannan suka jero tare don fitowa daga d'akin, ai kuwa suka yi kici6is da Afrat za ta wuce, sai ko ta hau tafi raf! raf!! raf!!! Tana fad'in mummy don Allah yi sauri ki zo ki ga mutanen ki. kai sisto, kin ga yadda kuka yi matuk'ar dacewa?? Let me give you a snap, sai kuma ta ce "af! ashe wayar ma yana parlour. Bari na yi sauri na d'auko phone d'in, sai ta juya da sauri, dariya suka yi sosai Arfat ta ce "kai Afrat ba dama, sai mu yi ta jiranta fa take nufi,Abeed ya ce "ni kai na sai na ga hoton zai bada meaning, kawai mu jirata, Jan hannunsa Arfat ta yi, tana cewa mu je ni dai don ina da abin yi. A kwana a tashi, ba wuya wurin Allah, ga shi har an shiga satin bikin su Arfat, tun farkon satin ake shagali iri_iri, don ayi events kala_kala wasu ma ba mu ta6a Jin sunan su ba, har kawo yau da dubun dubatar al'umma suka shaida daurin auren ABEED & ARFAT akan sadaki 50k. Dare na yi aka sada amarya da tamfatsetsen gidanta mai kama da aljannar duniya, k'arfe goma angon ya shigo da abokansa akayi sayen baki na alada aka bar ango da Amaryar sa,ya umurceta da si tashi, suka gabatar da nafila, sannan ango ya ciyar da amaryarsa, shima ya ci, suka yi hani'an, sai ga ni muka yi Abeed ya nufo inda muke la6e ya ce "don Allah ku fita haka, d'aukan rahoton kuma ya isa haka, wanda kuka yi a baya ma ya yi yan sa ido kawai , sai dai mu ce “Allah ya saka da alkhairi." Ba shiri muka fito muka yi waje Jabo sai Harare hararee takeyi, tun daga lokacin ba mu kuma waiwayarsu ba sai bayan 1yr, ko da muka je mun tarar da Arfat da katon cikin, haihuwa ko yau ko gobe. Daga nan gidan su mummy muka je, don ganin a wani hali su ke, abin mamaki, sai muka tarar da mummy da ciki, katoton gaske don har ya fi, na Arfat girma. Bayan sati da zuwan mu mummy ta haihu ta samu babies d'in ta twins, mace da namiji, kyawawan gaske, washe gari Arfat ta haihu ita ma, ta samu baby boy, mai kama da Abeed sak, murna a wurin wannan familyn ba a magana. Don sadakar da Daddy ya yi Allah kad'ai ya San iyakarta, don taron sunan ma hadewa aka yi, an yi k'ayatacciyar walima, don nuna godiar su ga Allah, don kuwa naira ta yi kuka da Idonta. 4 month letter, Abeed muka hango da shi da Arfat, a zaune a garden d'in gidansu, suna huta, shi kuma babynsu mai amsa sunan SULTAN, (kasancewar sunan Daddy aka saka masa) shi yasa suke kiransa da SULTAN, yana zaune a kyakkyawar walker d'in sa. Arfat ta zuba masa ido tana kallonsa, Abeed ne ya matso in da take, ya hure mata ido da iskar bakinsa, sannan ta sauke ajiyar zuciya, ya ce "babyna wai mai yasa me ki ne??? Tun dazu sai kallon SULTAN kike yi, ko ya chanza miki ne?? Murmushi ta yi ta ce "wallahi kawai ina tunanin yanzu yaron nan mallakin mu ne, sai na ji kamar a mafarki." Dariya Abeed ya yi sosai ya ce "wato yanzu wahala ta wuce, sai dadi, a lokacin da kina labour, har wasiyya kin ba ni, a zaton ki mutuwa za ki yi. Ya cigaba da fad'in "Arfat please ko nan gaba ki daina yawan fad'ar mutuwa, Allah hankalina ya matukar tashi, idan kin anbaci kalmar mutuwa akanki, I know mutuwa dole ce, amma yanzu zuciyata ta gama aminta da ke, ke kad'ai ce burina, sai babyn mu and wasu kids d'in da na ke saran za ki haifa mun nan gaba, babu wata mace da zata kai ki k'ima a idona, it will be an empty world without you, my everlasting wife". K'ank'ame shi Arfat ta yi, Tana fad'in "haba hubbyna na ce kadai na fad'ar wannan maganar dukan mu fa marayu ne, I give you my words, bazan ta6a barinka ba matukar ina numfashi a doron k'asa. Rungumeta Abeed ya yi tsam a jikin sa, yana cewa na gode, k'anwata, Allah ya ba mu tsawon kwana mai amfani tare da zuri'a d'ayyaba, a tare suka ce ameen, tare da sakin Murmushi. TAMMAT BIHAMDULILLAH! Anan muka sauke wannan littafin, muna fatan Allah ya yafe mana kurakuran da muka yi abisa rashin sa ni, ko kuma ajizanci na d'an Adam. Luv u ol our fans 😘😍😘 Maman Twins😍 da Hauwa M Jabo ke muku fatan alkhairi 🍃 adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *