Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Friday, February 3, 2017

AURE KOH ZAMAN GIDA? COMPLETE

adsense here akan hanyar asibiti nida qawata zeenah khalifa zamuje duba wata maqociyarmu da batada lafiya,Muna shiga asibiti mukayi karo da wata mata da yara guda biyu a hannunta zenah khalifa tayi sokoko tana kallonta.Ke zeenah khalifa kinji haushi ki kalli maza ki kalli mata.! Banason wulaqanci hauwa jabo.! Mikike nufi da inkalli mata in kalli maza? kamar wata bunsura..!!! Na kwashe dadariya nace yanzu dai yimin bayani mi kika hango.?? Ta kwashe da dariya kibari kawai,Hauwa jabo matar nan ta hadu billahillazi..Da ace ba baqa bace sai ince wllhy ba indiyace keni muje muyi qawance da ita,Ke zainab muna fama da talaucinmu zamuje gurin masu kudi.? Bazanje a wulaqantaniba gaskiya,Ke Hauwa jabo wllhy kin cika tsoro,Idan bazakiba bari inje ingabatarda kaina,Ta kwace wayata taje tana kuri. Bansan yanda sukayiba naga har sunyi musanyar number suna yiwa juna murmushi wani namiji yazo naga yana mata magana tay murmushi ya rungumeta hannunsa dayan hannunsa riqe da handbag dinta ya mata kiss a kumatu ina tsaye ina kallo araina nace dama matan nigeria suna soyayyah haka? In shot sun burgeni kuma inason inji tarihinsu da inda suka iya soyayyah irinta Iranian saboda Iranian ne kawai zakiga sundaukarwa matansu jaka su rungume jariri kuma su rungume matar kamar wani zai kwace musu.. !Zainb ta dawo sai murna takeyi ina tsaye,Sai wangale baki takeyi zainab,Amma fa matar ta haduko H jabo? uhun ba laifi!, Ke Wllhy kincika matsala,! Nidai muje, Zamu shiga kenan sai gasu sun fito suna dagawa zainab hannu sai wangale baki take har yar wushiryarta da dan dimple dinda take kuri dashi ya fito araina nace zainb ansamu aikin yi, Munshiga mun duba mara lafiya munfito muka wuce city plaza muka dan sayi ice cream muka samu keke npn sai gida..... Eshqi mano too... tuye qalbam mimune....zandagi batu behtare..... Ringtone din zainb kenan kuma gashi tashiga wanka naga anrubuta sister zainb araina nace waye kuma sister zainb... hello, hello namesake, nasissim adaya banqaren naji dafada cike da dariya... Araina nace wannan yar turkiyace ni jabo ba Turkish na iyaba hakadai na amsa mata nasissim eyem ebit ta kwashe da dariya.. Araina nace zatace ban iyaba na kwabsa, Sai tace ni ban iya wannan da kika fadaba nima nay dariya, Tace yaushe zaku zo gidana da sauri nace gobe zamuzo ba matsala, Eh kuzo ta fada cike da shauqi, Ta bani address dinta na rubuta zeenah khalifa na fitowa nace namesake dinki takira tace gobe muzo... ihuuuuuuhw.!! Wani ihu tayi tanajin dadi nima naji dadi ko banxa inason muje inyo gulma... Tun safe kinsan yau zamuje unguwa ko? Unguwa kuma.? Lallai wllhy jabo kinji dadinki kin manta zamuje gidan namesake dina.!!?? Au natuna qarfe nawa ma zamuje.?? 12 mukace mata. Kk.. mun isa gidanta wani qaton gidane da shuke shuke ya rufe ko ina nace anya nanne zainb karmuje a cire mana kai, Eh nanne mana muka danna bell maigadi yabude mana yace su zainb ko mukace eh kushigo, Araina nace har angayawa maigadi zamuzo Lallai anaji damu.. Munsameta tsakiyar gida tana ganinmu tazo ta rungume mu...... muje zuwa muji yanda hauwa jabo zatayo mana gulma agurin zainab...... Kukasance tare dani a AURE KO ZAMAN GIDA part ♥♥♥AURE KO ZAMAN GIDA♥♥♥•••••••• •••••••PART 2•••••••••••••••••• …Munci munsha mun hole anan na fahinci zainab tanada balaeen saurin sabo kuma akwai tsiwa da wasan rainin hankali, Nandanan muka saba da ita amma naga tafi maida hankali gurina ko dan taga nafi hankaline ohoo..? Watannmu uku da sanin zainab duk ansanmu a gidanta tana zuwa gidanmu sosai,Ranar munje gidanta, Nan nanemi ta bamu labarinta daga farko tayi gardama daga baya mitayi tunani ta amince naso inyi shishigi intambayeta amma sunyi rayuwa a iran ko amma sai nafasa nace bari in barta kawai maji daga baya... Tun safee nazo inji gulma nikadai nazo saboda nasan idan nazo da zeenah khalifa to labarin bazaimun dadiba, Nayi sa'a tagama aikinta gaskiya zainab tanada kazar kazar batada son jiki ko kadan, Takawomin fresh milk nashanye, Ta gyara zama ta fara bani labari kamar haka......... Sunana zainab Abdullahi mahaifiyata gurin hai huwata Allah yamata cikawa, Mahaifina mutum ne mara kulawa sosai, Sam bai damu da tarbiyarmu ba baidamu da chin muba bai damu da shanmuba, Gamu mu mu shida ne a gidan ni kadai nake agun mamata data rasu sauran biyar din duk yayan kishiyar mamanmune maza uku mata biyu,Agurin kishiyar mamata na girma, kishiyar mamata mutumce wacce batayi dan Allah idan kikayi mata zata miki idan baki mataba to bazatayi mikiba,Amma bata cutar da kai sai ka cutar da ita, Tana dauramin tallan kayan miya ranar da nasiyar to zamuji dadi idan kuwa yayi kwantai to bamu ba abinci sam saboda da dan ribar da take samune take bamu abincin safe dana rana, Nadare kuwa baba yake bayarwa, Bata ta6a dukanaba kuma bata cika yimin fadaba amma tanacin uban yayanta sosai nice babba agidan, Banta6a sanin hanyar makarantar bokoba balle ta addini har nakai shekara goma sha daya bana karatu sai yawon talla, Ina sha'awar boko sosai inada wata qawa wacce muke yawon talla tare da ita amina s bawa, Ita tana dan boko ta bani littafinta daya tafara koyamin A B C D.... Ina ganewa sosai saboda inada hazaqa duk ranarda muka saida kayan miya da wuri to ranar zamu zauna muyi boko wasa wasa har nafi amina iya karatu sai tafara jin haushi saboda musun da nake mata akan wannan haka yake tace a'a ba haka yakeba, Haka yake tadaina koyamin komai ataqaice duk wata takardar qosai ta unguwarmu idan nagani sai nakaranta na iya hada kalmomin english inkaranta amma bansan ma'anarsuba ke intaqaita miki jabo duk wani karatun indai karantawane ina iyayi da rubutawa..... Akwai wata rana na fito tallan wara saboda yanzu nadaina tallan kayan miya wara nake talla yafi kasuwa ina tafiya naga wata qatuwar mota baqa baka ganin waye aciki,Anyi parking dinta a gefen hanya, Kusan wata daya Kullum sainaga motarnan wani yaro yace wai mai motan yace ki kawo wara na kalli motan lokacin iya tunanina nasan mai Wannan qatuwar mota bazai ci waraba, Nace bazanje, Shegiya matsiyaciya arziki yana kiranki kina gudu kar kije miya dameni wannan mutumin duka yake siya yace kikai masallaci.... kukasance tare dani a AURE KO ZAMAN GIDA part 3 ♥♥♥AURE KO ZAMAN GIDA♥♥♥•••••••• ••••••PART 3•••••••••• …Abinda yasa naqi zuwa kuwa kiranshi maman jamila (kishiyar maman mu) tace koda ban saida tallan da ta dauramin ba kada in kuskura wani ya bani kudi yamun juye ko in bishi gida duk ranarda nayi haka sai ta yankani,Kuma zata riqa dukana kamar yanda take dukansu jamila (yayanta kenan )Ashe su jamila juye suke ana ta6a lalubarsu shiyasa take chin ubansu.. naceto, Zo karakani muje tare har yace bazai jeba sai kuma yace kawo inkaimuki na bashi ya kai ya dawo yace waranki na dari shida da talatinne ga kudin kikai wa almajirai waran. Yace min ko ki saida rabi kikaiwa almajirai rabi ki boye sauran kudin. Har na yarda da shawaransa sai kawai naga idan maman jamila tagane zataci ubana tace ina nake samun kudi, Nakoma gida da wuri akace ya akayi nadawo da wuri nayi bayani tace kar dai in kuskura in shiga motarsa kuma duk abinda ya bani kar inci, Nace to, Tun daga ranar idan nafito talla nan zan tarar da motar mutuminnan nan kuma zan barta, Banta6a zuwa jikin motanba sai na jira audu abokin tallana yazo yakai asaye abani kudi... Yanzu babana ya chanza yana bamu kulawa sosai kuma ya sakamu islamiya dukanmu, Inada qoqari sosai amma su jamila sai a hankali cikin shekara daya na sauke qur'ani nashiga bangaren hadda,Namma banyi qasa a guywaba wata tara na haddace qur'ani da tajwid da komai, Nice tafarko atarihin makarantarmu da ta haddace qur'ani cikin wata tara dama tun lokacinda nake karatu kamin in iya na haddace shiyasa da nazo sai yamin sauqi nandanan na haddace, Akayi gagarumin bukin yaye dalibai hadda shugaban makarantarmu yazo nay karatu da muryar nan tawa nasamu kyaututuka sosai agurin malamanmu da manyan baqi, Yanzu na daina talla saboda baba yana iya bakin qoqarinsa yachanza sosai yanzu baya barinmu da tsumma kamar da mun wadata sosai, Ranar nadawo daga islamiya baba yace inzo naje gunsa sai yacemun wai aure zai nida ko nono banida za'ayimin aure gani da qaramin jiki saboda ta dade da fara nono amma ni yar qwaila dani, Bance komaiba nace to, ko kinada wanda kikeso nace a'ah, Aka sa ranar aurena aka dauramin aure da mijin da banta6a ganiba bansan ko waye shiba… Kukasance tare dani a AURE KO ZAMAN GIDA part 4 ♥♥♥AURE KO ZAMAN GIDA♥♥♥°°°°°°°°°°° °PART 4°°°°°°°°° …Iya tunanina aurena da wani dan mashukurin mai kudi rana daya akayi shi dan jama'ar da suka taru sunfi qarfin suzo aurena amma daga qarshe mungane gurin auren nawa sukazo,Har bayan daurin aurena ina gidanmuban tareba, Bana fita ko ina, Sai taya maman jamila aiki, Ke in gayamaki jabo wllhy saida nayi shekara biyar agidanmu ba miji ba labarinsa kuma ba zancen tarewa, Har na balaga, Ba miji inason inyi magana amma kunya ta hanani yin magana duk qannena mata jamila da hafsatu an musu aure jamila da wani har ta haihu da wani ciki ajikinta hafsatu kuma da cikinta tsoho, Nigani agida farko abin baya damuna kuma sam ban fuskantar tsangwama agurin maman jamila, Yanzu na girma nasan miye aure saboda ina zuwa wata islamiya dadare ta matan aure a unguwarmu, Inajin abubuwan da ake koya mana mata da wuri suke zuwa dan suyi ta tadi, Mijina kaza mijina kaza nidai bana ce musu komai, Abin duniya ya isheni nayanke shawarar zan yiwa baba magana sai dai kuma kunya nakeji nace ko infara yiwa maman jamila maganane inji abinda zatace, Haka kuwa akayi, Ina biya mata karatun qur'ani bayan munqare muna hira saina cemata wai maman jamila waye mijina..? Naji kamar bata jini ba namaimata tambayar, Ta d'ago ido ta kalleni tace mun kitambayi babanki, Nayi shiru, Ban qara cewa komaiba, Munqare karatu da ita na shige daki, Sai tunani kala kala nakeyi gaskiya inason sanin miye matsayina matar aure ko bazawara? Zaman aure nake ko zaman gida? Shekara biyar ba miji ba labarinsa sai wani niqab da baba yasani sakawa tunda aka dauramin aure, Yan kwanakinnan nashiga damuwa sosai sai nake tunanin ko dan banida uwane aka yimin haka, Lallai maraici hadarine, Nashiga rera kuka mara sauti nayi wata biyu Kullum sai nayi kuka duk wata walwala ta gushe mini banida aiki sai tunani da damuwa nashiga tsaka mai wuya narame, Na kode, Nayi baqi, Duk wata halitta ta jikina saida ta chanza.. Na yi alwashin zanyiwa babana magana, Bayan yadawo daga kasuwa nace inada magana dashi yace to naje gurinsa, Inson inyi magana sai muryata ta fara rawa bansan lokacinda kuka ya subucemin ba nayi kuka sosai baba ya rasa gane kaina gashi ba kowa agidan saini nima dan banje islamiya bane, Daqyar nasamu nayi shiru amma nakasa tambayarsa, Can baba yace nasan zaki damu ace shekara biyar da watanni da daura miki aure amma bakisan mijinkiba.! kuma baki tare Gidankiba ba ,Amma kiyi haquri nasan banmiki adalciba, Nafarko ban baki damar zabar mijin da ranki yakesoba ban tambayi ra'ayinkiba inji shin kina sonsa ko yaya,! Bakisan wayeba bakisan komai akansaba hasalima bakisan wayeshiba ban barki kinyi karatun bokoba, Sannan shekara biyar dai dai da rana daya bakimin magana ba Allah yayi miki albarka kuma mijinki wannan shekarar zai dawo insha Allah, Idan ya dawo tare gidanki tashi kije ki kwanta Allah yayi miki albarka, Koba komai raina yayi sanyi najin cewa mijina zai dawo wannan shekaran dan wllhy na gaji da zama da igiyar aure akaina… Kukasance tare dani a AURE KO ZAMAN GIDA part 5 ♥♥♥AURE KO ZAMAN GIDA♥♥♥•••••••• •••••PART 5••••••••• …Na rogi alfarmar baba ya barni in riqa zuwa wata yar makaranta da ake lesson anan qasa da gidanmu baba ya amince, Kuma yace inci gaba da kare mutuncina, Nafara zuwa lesson abubuwa da yawa nasan sunansu amma bansan ma'anarsuba malamin da yaga inada hazaqa sosai sai ya bani kyautar wani littafi sunayen abubuwa da hotonsu cikin sati daya na haddace su duka dama nasan sunayen abubuwan kawai bansan sunayensubane sai yanzu, Ahankali nafara iya magana da english cikin wata biyu.. Hauwa jabo ko kin gaji mu bari sai gobe nace a'ah muci gaba kawai, Tayi murmushi taci gaba.... Ranar nadawo daga lesson dina tun zauren gidanmu naji wani qamshin turare mai rudarwa qamshi sosai naji wata sassanyar murya ana wani yare bansan mi suke cewaba a lokacin (to namifahmi hamun juri k to hamsari man hasti uwn ham hamsari mani to modare bachem hasti, chira mutawajji nisti ) adaidai lokacin nabi gefensa na wuce fuskansa na kallon yamma so baisan nashigoba na shigo tsakar gida natararda baba fuskarsa cike da fara'a nima nayi murmushi nace baba miya faru naganku kuna jin dadi yace ABDUL AZEEZ ne yadawo.Waye kuma abdul azeez baba? mijinkine, mijina? Eh Sai ban sake cewa komaiba yayiwa su baba sayayah sosai ina tsaye ina kallonsu, Na wuce dakina nan natarar da kaya niqi niqi naci dana sha dana shafawa tufafi kala kala turaruka kala kala na kira maman jamila na nuna mata tatayani buda wasu naji dadin kayan koba komai nasan wanda yasiyo kayan mai kudine, Wasu kayan irin na qasar wajene bana nigeria bane hadda waya a cikin kayana (LG G Flex) wayan ta hadu iya haduwa sai wani envelope nagane wasiqace naqi budawa saida maman jamila ta fita .... Hello my wife Sai kuma number sa daya rubuta a qasa banta6a ganin letter irin wannan ba, Naji dadi koba komai nasan cewa inada miji, Tun safee baba ya kirani yace in kunna wayan da aka bani na kuwa kunna ko minti hudu ba'ayiba kira yashigo naga ansaka AZEEZ nidai bansan ko wayeba na dauki wayan nayi sallama ingayamiki jabo bai amsaba saida nayi sallama biyar ba amsa nayta danne danne har na gane yanda ake kashewa karo na biyu ya sake kira na dauka namma ba magana nasake kashewa karo na na uku naqi dauka har ta qare ringing ya turo sms (I luv d way u r talk,ur voice is agreeable ) Kwana shida da dawowar azeez aka fara shirye shiryen tarewana anyi min duk abubuwan da suka kamata maman jamila ta gyarani iya qoqarinta, Aka kaini gidan mijina in taqaitamiki labari, H jabo saida nayi wata shida cur agidan nan bansaka Abdul azeez a idonaba komai na gidan ya wadata ba abinda nake nema, Duk sati za'a kawo min cefane da kudi ko zan buqata kuma aka bani mota da driver duk inda nakeson zuwa akaini, Ingayamiki jabo saida na gwammace zama gida da zaman gidan aure, Rayuwa ta sauya bana zuwa ko ina sai gida zubi zubi tun inajin tsoro har nadaina jin tsoro nabarwa Allah komai, Nayi magana da malaminmu mai mana lesson akan yasamomin wanda zai riqa zuwa gida yana mini lesson, Yasamomin wata mata tana koyamin dan science da wasu subject na seconds skul naba kaina wahala sosai wajen ganin na iya karatun science Kullum ina duba internet ina daukar lecture a internet malamar har mamakin basirana takeyi dan kuwa har tamun hanya inje in zana waec idan naci zata nemamin admission a university dinsu, Sai da na zana waec naci ina zancen zuwa kenan sai ga saqo daga mijina inje za'amun international passport, Wata mata takaini immigration office akamin passport aka kar6o min ticket da visa na barin qasa..… Kukasance tare dani a AURE KO XAMAN GIDA part ♥♥♥AURE KO ZAMAN GIDA♥♥♥★★★★★★PART 6★★★★★…Wai ashe jabo duk zaman da nakeyi. Abdul azeez baya nigeria gabaki daya yana iran abinshi, Ni ya zan bar wata qasa ni kadai alhalin ban banta6a zuwa koda airport ba, Haka nayi kuka nayi bankwana da yan uwana dan bantabm6a tunanin zan dawoba nashiga mota sai kaduna, Ina ganin jirgi jikina ya mutu na tabbatarda bazanyi raiba matsawar na hau wannan gangaramar, Wasu zafafan hawaye suka zubomin tunda nashiga jirgi nake kuka har muka isa Lagos, Daga lagos zamuyi fly 6:30 har aka gama shiga jirgi ban saniba saida wata mata tamun magana sannan nagane cewa jirginmu saura 7mnt ya tashi tataimakamin nasamu nashiga jirgi ina shiga idon kowa akaina har ina tuntu6e nazauna ga fitsari inaji ina tsoron tashi, Da ya matseni haka nan na lalla6a naje nayi amma ba ruwan tsarki naga zan batawa kaina lokaci nasaka tissue na goge na fito, A daddafe muka isa Beirut a Lebanon kenan, Na sake shiga wani jirgi sai emirate dubai kenan, Nasha kallo a dubai qasar ta burgeni sosan gaske a dubai nasamu transit 18 hrs wllhy haka na zauna a airport ga yunwa kamar zata kasheni na daddafa naje naci wani abinci $50 bangane komaiba ba dadi sai dan banzan tsami nayita amai sai zazza6i anan bacci yayi awon gaba dani ban farkaba sai 9:12 kuma 8:30 zamuyi fly ataqaice nayi missing din fly naci kuka har na gode Allah naje gun ma'aikatan gun namusu bayani sukace jirgina ya wuce sai na sake sabon bucking suka min komai da komai, Ina nan zaune abin tausayi sai ga wata mata da mijinta zasuje iran kuma hausawa ai kamar ansakani aljanna haka naji nadan gaya musu yanda akayi nayi missing din fly sukaita dariya nima saina wayance nayi dariya amma nasan sungane ni dibgaggiyar local ce ni, Dan kuwa kina ganina kinsan sai a slow ko a shigata, Sun taimakamin mun isa iran nanma nayi wani qauyanci dan kuwa anbani number akace idan na iso airport din tehran inyi waya sai kawai nabaiwa maman nargees kudi nace ta siyamin ticket nabisu garinsu mashhad saida muka isa maman nargess tasiyomin sim card nasaka nakira numbar da aka bani, Nayi sallama aka amsa da wata sassanyar murna mai ratsa jiki dajin muryar nagane cewa antsorata ana tunanin na6atane kina ina yanzu,? Airport kisamu wani mutum cikin ma'aikatan gurin inyi magana dashi nasamu wani mutum na bashi yagayawa. Abdul azeez cewa ina mashhad, Yaji haushi sosai kaman in kar6i wayaya kashe nakira ba'adauka qarshe ya kashe wayanshi natsorata sosai naje gun wani mutumi shi ba England ba sai surutu daga wata gasa nake (az kuzo omadid ) Ni ba gane yarensu nakeba su kuma ba wani gwagwaran turanci ba haka dai nasamu har ya gane me nake nufi ya siyamin wani ticket daga mashhad zuwa tehran inkoma inda nafito yamun komai mutanen gasar iran akwai tsoron Allah tare dasu ga kuma amana natashi nakoma tehran ina isa nasake kiranshi naji wayan akashe can naji wayan yayi ringing na dauka kina ina? Nadawo airport dinda na sauka daga farko yayi shiru ina hello naji shiru sai na kashe wayan ashe wai ya biyonine ni kuma nakoma garin haka na qama zama a airport ga qasar da wani mahaukacin sanyi wayata ta mutu nasamu wani mutum ya nuna min masallaci nayi sallolin da ake bina nasaka chaji sai bacci da gurin akwai dumi ban farkaba sai asuba shima yanwa ta tayar dani ina duba wayana naga 38 miss call. Banji haushiba nayi sallah asuba na tashi na nemi gurin chin abinci ina chin abinci naji ance min ke.!!… Kukasance tare dani a AURE KO ZAMAN GIDA part 7 ♣♣♣AURE KO ZAMAN GIDA♣♣♣:::::::: :::::::::::PART 7:::::::::::::::: …Ban waigibo hasalima banjishiba saboda na tafi duniyar tunani, zainab ce.?? Na waigo sai naga wani kyakyawan mutum dogo fari tareda yan sanda guda biyu, Sukayi yare sai naga sun juya suntafi, Ina dago kaina ya kwasheni da wani wawan mari saida na fadi qasa, Anan nace Lallai ma mutuminnan dan iskane ya aureni ya ajiyeni gidan ubana shekara biyar, Sannan yakawoni gidansa wata tara, Ba kulawa, Yaturoni daga qasa zuwa qasa ni kadai saida na hau mutuwa(jirgi) sau shida sannan inyi kwana hudu ina garari qasa da qasa inzo ya rasa mizai sakamin dashi sai mari gashi banida lafiya , za'ayi ta kuwa dan wllhy sai ya sakeni yanzu kuma ya maidani gidan ubana nagaji da Wannan bala'een tun banida wayo nake hadiyar baqin cikin sa har yanzu na tashi na dauki wayata naja kujera na zauna, Bai min maganaba yaja hand lgt dina ya tafi yana jiran in biyoshi nayi banza dashi, Shiru sai da yakai gate din fita yaga bani ya dawo, Na daura kaina akan table din gurin ina kuka yazo ya ta6ani ban motsaba ya girgizani ya matso kusa dani yace kizo muje gida, Wani dum naji, Araina nace dan yasan muryarsa tanada dadine shiyasa baya magana, Ashe duk abinda mukeyi a police din gurin suna kallonmu a cameran dakinsu yazauna bai sake maganaba sai ga yan sanda sunzo suka ja shi gefe suka tattauna suka dawo police yacemin (he is ur husband?) Araina nace inaga mutanen wannan qasar basu iya turanciba sai yarensu, Nace masa (no he is nt my husband ) Ya zare ido ya kalleni da idonsa, Nasaukar da nawa idon, Suka sakeyin yare police ya qara tambayata mijinkine nace musu a'ah, Suka jamu mukaje wani daki suka fara masa question wai idan matarsace ina certificate din auren mu? Nan yayi turus baisan nigeria basa wani certificate ba nan nafahinci bayason magana sosai duk yarasa mezai musu, Suka kar6i passport dina sukaga sunana da sunansa suka kar6i passport dina da nashi sukace mutafi kamin suyi bincike,Intashi muje na sake fashewa da kuka, Yayi bala'een daure fuska yayi musu yare sosai sai ya miqa min hannu na kalli yanda ya daure fuska na saduda na miqa masa yamatse sosai ya jawo jikinsa ya rungumeni na natsu sosai ban ji komai a rungumar da yamunba saboda ina masa kallon azzalumine kuma ga tsoronsa da ya kamani sai qamshin turarensa da yake dukan hanchina, Mukaje yatari taxi muka shiga munyi tafiya sosai sannan muka isa inda zamuje muna isa ya bani key yace ga gidanki nan. Tofa… Kukasance tare danu a AURE KO ZAMAN GIDA part 8 ♦♦♦AURE KO ZAMAN GIDA♦♦♦°°°°°°°°° °PART 8°°°°°°°°°° Miyake nufi da ga gidananan yana nufin ya tafi kenan wani sabon kuka nafarayi ga sanyi inaji harna tashin hankali amma ba yanda zanyi naduba gabas da yamma ba wani mutum na lalla6a na bude gidan nashiga gidan qaramine zaman mutum daya na zauna nayi kuka har na gode Allah ga sanyi kamar me saboda anyi snow sosai gashi ni bansan yanda ake kunna heater room ba danaga zan mutu da sanyi natare kitchen da zama, Wato ya raboni da iyayena yakawoninan dan yaudara garama nigeria ina ganin iyayena idan naso ganinsu amma yanzu idan naso ganinsu sai na kashe over half million sannan zangansu, Lallai ina cikin tashin hankali mara iyaaka, Satina uku bansakashi a idonaba narame nadaina chin abinchi ranar naji hayaniya ashe maqociyatace mijinta ya rasu naje sunata kuka sun bani tausayi talakawane ba laifi yar budurwar yarta tana gane English kadan kadan shima idan ta kwa6a sai cikin mutum yayi ciwo kan dariya, Ahankali nasaba dasu sosai suna koyamin yare kadan cikin sati biyu nafara fahimta Abdul azeez kullum sai yamun sms ya nake amma bana bashi amsa wai ashe akwai camera a gidan wacce duk wani motsina yana gani a gidanshi shiyasa yashareni watana uku bansakashi a idoba na yanke hukuncin komawa gidan su makwabciyarmu da zama tunda yanzu nasaba dasu sosai kuma batada yaro namiji a yaranta mata biyune. Na kashe wutar gidan gaba daya na tafi abina yare kam alhamdu lillah nagama iyashi tsab, Nagayawa mai kawomin kayan abinci idan ya kawo min kayan abinci nan gidan zai kawowa komai nawa nan nake yinsa arayuwa kwata kwata namanta da abdul azeez hankalina kwance nakashe banzar wayar da yakemin sms, Ashe yayi tafiyane shima shiyasa bayi gane bana gidanba yaje Turkey wani aiki na wata daya yadawo ya kunna cameransa yaga wayam basa aiki anma kasheshe gaba daya yayi forwarding din karsheb zamanta gidan yaga tana hada kaya da komai dakomai ta kashe wuta yaji tsoron ko ta gudu ya tuna passport dinta na hannunsa hankalinsa yayi bala'een tashi bashiri ya dawo gida qofa a gargame nan ya zauna ya fara danasanin abinda ya aikata tabbas bai yiwa zainab adalciba koda yasan shi yayiwa matarsa alqawarin bazai kula wata maceba matsawar tana raye, Zainab itace za6insa tun tana yar shekara 9 yanemi aurenta aka bashi ita, Itace za6insa, Ita yakeso, Dan yanasonta ya aureta, Ya auretane dan kar wani ya gwace masa ita yasata zaman kulli shekara hudu ya ajiyeta gidansa a naija wata tara ya kawota qasar da batada kowa batasan kowaba ya tafi ya barta yana ganin halinda take ciki amma dan kar ya batawa matarsa uwar yayansa rai yaqi za6insa wacce sonta yake neman kasheshi, Yamanta itama zata haifamasa yarane, Yanzu ina zai sameta..? Ina zuwa zainab kina nufin Abdul azeez mijinki yanada wata mata?? Kibari kawai wllhy mata harda yaro daya inna lillahi wa inna ilaihi rajiun... Hauwa jabo muje muyi sallah mudawo in qarasa miki.… Kukasance tare dani a AURE KO ZAMAN GIDA part 9 ♥♥♥AURE KO ZAMAN GIDA♥♥♥°°°°°°°°°° °PART 9°°°°°°°° Jikina a mace nayi sallah dan abin ya dauremin kai jin cewa azeez yanada mata harda yaro, Muci abinci sai muci gaba ko jabo nace ai ina azumi ta kwashe da dariya, kinmanta kinsha fresh milk dazu nima abin ya bani dariya dan kawai insha labari nace ina azumi tamana girki indomie mukaci a gurguje taci gaba da bani labari... In gayamiki jabo kamar ance fito dan ba inda nake zuwa sai wani park na bayan gidana shima mutane suka fara damuna suna cemin (siya pust)Baqar fata kenan nadaina zuwa ina gida abina ina fitowa naganshi zaune dirshan cikin sanyi yana kuka wllhy jabo ko kwaya zarra banji ya bani tausayiba hasalima wani tsanarsa da nayi duk lokacin bansan yanada mataba, Ina kallonsa miyaji sai naga ya daga kai da qarfi ya kalloni hadi da wata irin kyakyawar aziyar zuciya, Ya miqe tsaye ya bude qofar gidan ya shiga kai tsaye na koma inda nake har magriba ban shigo gunsaba nama manta dashi inachan gurin makwabtana yar tsohuwa dai tagane akwai wani abu (chi shod dokhtaram?) Miyake faruwa yata ( hech) ba komai (pas chira shoharat omada wali to khushhal na shodi ?)To miyasa mijinki yazo bakiyi murnaba(Hech momon alan miram pishash)Ba komai mama yanzu zanje gurinsa(Affarein dokhtari khub zud baro guna dore az rahi dur omade istiqbalash ham na karde)Da kyau yata yi sauri kije, Bazaiji dadiba ace yadawo daga tafiya amma kinqi kije tarbarsa, (Boshe momon)To mama. Na fito sumi sumi na shigo a parlour naganshi zaune yayi wujiga wujiga dashi ya kalleni ina shigowa ya miqe tsaye naja natsaya na dauka zai kwasheni da wani marine kamar yanda yayimin a airport, Amma sai naga sa6anin haka, Durqusawa yayi gabana yana kuka kaman qaramin yaro yana bani haquri ya cutar dani yayita surutansa har yagama bance masa komaiba, Yatashi yagoge fuskarsa wai inshirya zai maidani wurin aikinsa nanfa aka fara sabuwar rigima dan bazan yarda yakaini wani sabon guri ya ajiyeniba alhalin bansan kowa agurinba, Nan nashiga rera kuka yazo yana lallashina amma naqiyin shiru, Yayi yayi naqiyin shiru sai shima ya zauna ya fara kuka lokacin abin ya bani mamaki ace kamarsa yana kuka sai ya bani tausayi ahankali na daina kukan natashi na bashi guri intaqaita miki jabo saida yayi nasarar barin wannan gidan dani... Kukasance tare dani a AURE KO ZAMAN GIDA part 10 ♥♥♥AURE KO ZAMAN GIDA♥♥♥<×><×><× >PART 10<×><×><×> Nayi kewar maman sumayyah maqociyata sosai amma yana iya sai haquri, Zamana dasu na waye sosai kuma nayi clean coz sumayya yarta yar duniyace irin shigar datake agida da yanda take hulda da mutane nima na koya dama nima ba bayaba gurin shed'ana lokacin idan kika ganni sai kince nayi karatu ne wata university jabo.... Mun isa gidan da zamu zauna, Gida qaton gaske yanada part biyu a dayan gefe muka wuce da kayana gidan yaci uban gidan da na zauna sau dubu, A parlour na zauna fuskata a daure yaqare gyara komai ya siyomin pizza inajin yunwa dole naci, Yazo yazauna yaci gaba da bani haquri har ya gaba ban ce mishi komaiba, Ina kwance ina game da wayata najiyo hayaniya awaje kuma ga dukkan alamu da hausa ake fadan hayiniyar tayi yawa kamar ma gidana ake yinta ina fitowa nayi karo da wata mata yar lukuta da ita dan takaiki jabo an, Ina zuwa abdul azeez yachanza yare yakoma farsi yace (turu khuda ba zabani khudamun juluyesh harf nazan namikhom alan bi fahme)Dan Allah karkiyi magana da hausa dan banason yanzu ta gane abinda muke ciki, Matar itama da yaren tace (khub agyar nami khod bi fahme y kari kun)Idan bakason ta gane kasan yanda zakayi dani, Sukayi ta magan ganu da yare inajinsu basusan adaqe nake kallonsuba dan duk inajin abinda suke fadaba gashi batama iya yaren ba, Abin yabani dariya sosai yanda take cewa sai ya maidani inda yadau koni ita bazata zauna daniba, Araina nace nima bari in ta6a nawa iskanci dana koya agurin sumayyah, Na matso kusa dashi na rige hannunsa yanda koda yayi qoqarin kwacewa bazai iyaba nace masa eshqam (my dear ) Wannan matar da ka samo tazo tana mana haushi agida kaman karyafa?? Ta juyo da qarfi da daga hannu ta wankeni da wani wawan mari, Kaji tassss itama ya wanketa da mari nima na wanketa da mari sai tayi sololo tana kallonmu dan gaskiya ta mata yawa nima nasan nayi jarumta jabo, Dan matar agirme ta girmeni takai 34yrs fa nasaka hannuna na damana rungumeshi ta baya na kwanta a qirjinsa, Nace mata duk iskanchin da zakiyi karki kuskura kice zaki dagawa mijina hankali najawoshi shiko solon sai ya biyoni nashiga daki na kullu qofa ni na barta a parlour tana zage zage ta fasa abunda zata iya fasawa ta gaji ta tafi, Ingayamiki jabo tunda nashiga daki na wuce bayi na kulle kaina shiru har yakirani na kunna ruwa yaji qaran ruwa yasan dai cewa inajinsa yayi jira yayi buga gofa har ya gaji nayi banza dashi, Kinsan wannan matar wai matarsace ashe dama yayi aure har sunada yaro, Ke wllhy jabo haka nasamu kaina ina bala'een kishi da matarsa dukda nasan cewa banasonsa, Amma matar ta bani haushi, Nayi kuka har na nagaji, Nidai bansan bala'een da yake biye daniba niba uwaba dasai ingayamata haka nayi ta fama da baqin cikin kishiya amma duk da haka tsorona take dan duk bala'een da zatayi bata zuwa kusa dani saidai tayi nesa dani, Ataqaice ingayamiki hauwa jabo, Matarnan maza takebi ke hatta yaron da ta haifa ba na azeez bane kuma duk ni na ganesu, Yanda akayi kuwa shine.... Kukasance tare dani a AURE KO ZAMAN GIDA part 11 ♥♥♥AURE KO ZAMAN GIDA♥♥♥<<•>•<•> •>>PART 11<<•>•<•>> … Ina gaya miki jabo kullum idan abdul azeez ya fita sai tayi wata baquwa da qaton hijabinta kinsan Iranian akwai saka hijabi kaman larabawa to haka baquwarta take zuwa kullum, Kuma sai mijinta ya fita ranar ina wajen swimming pool ina kallon ruwa sai kawai naji maganar namiji amma da farsi suke magana tana cemishi.... Kaima kasan ina sonka kuma nafisonka akan Wannan mutumin wllhy abu kadan nake jira in kama gabana dan nagaji da zama dashi,Nidai duk wuya duk dadi karki manta dani kinsan idan baki bazan iya rayuwa ba, Duk wannan maganar da yaren farsi sukeyi, Basusan inajinsuba, Abinda yasa ban gara tantacewaba kuwa shi yaren farsi bashida mace ba namiji suna zuwa tace mishi karyayi magana ga yar iskar yarinyar nan sukayi dariya a hankali suka wuce kinga zargi bashida kyau jabo, So banyi saurin zarginsuba duk da haka amma abin ya dauremin kai matuqa dan kuwa muryan namiji sosai naji, Bayan kwana biyu yaqara zuwa ita kuma tadan fita sai nace masa batanan yayi kaman bayajin hausa inata magana ba amsa sai kawai namishi na kurame najawo hannunsa nashigo dashi sassana na zaunar dashi a parlour har tadawo, Tunda muka shigo parlour na yake bina da kallo duk inda nayi, Naji tsoro sosai dan kallon da yakemin kallon da saurayi yakema budurwarsane, Nashare kar yagane, Ya miqe tsaye yamin alamar zai tafi inda nayarda namijine takalminsa dana gani number 46 nasan ba qafar maccen da zata saka wannan takalmin nakwashe dadariya nashe da shigiyar qafa taki kamar ta masu kwasan kashi, Yajuyo ya kalleni rai abace amma baicemin komaiba na sake cewa kinsaka hijabi kin rufe rabin fuskarki kamar munafuka daganin yanda yakeyi nasan yanajin abinda nake cewa amma ba halin yamin magana asirinsa ya tono naqara cewa tsawo kamar palwaya nace duk mijin da ya aureki yayi asara mace kamar namiji ga munin bala'een dagani kin hada dangi da bare bare wannan uban muni haka kai amma duk yayi qawance dake yaji haushi itama maryam din asara ne yasa tayi qawance dake, Wannan magan ganun da nake masa inayine dan kawai yayi magana inji shin namijine ko mace amma yaqi yayi saima daure fuska da nayi muka kawo kofar shiga gidan ta nace mishi (khuda hafee) Sai anjima yanda nafada irin nayan koyo kar yayi tunanin na iya yaren, Yamin murmushi ya daga hannu araina nace kinga gardin banza wllhy wannan namijine kuma saina tona musu asiri abin duniya ya isheni sai wata dabara tazomin kamin suzo lambu suyi hira sai insaka wayata agurin inyi recording din abinda suke cewa hausa da farsi duk ina ganewa ranarda nasami abinda nakeso kuwa ranarda sukayi maganar cewa shi ya gaji gaskiya zai sace mustafa (sunan yaronta kenan) Dan yana buqatar dansa agidansa tanata faman roqon ya rufamata asiri har taqare hada dukiyarta sugudu tare sun saka ranar da zasu gudu nikuma nashirya tona musu asiri karkiyi tunani cewa wani abu yana shiga tsakanina da Abdul azeez aah ba komai tsakaninmu dashi sai sallama, Sai sannu da zuwa, Ranar da safee natashi yana fitowa nace masa inada magana dashi yau misalin qarfe biyu na rana yazo gida kuma banason idan zaizo yagayawa uwar yayansa zaizo kawai idan lokacinda nakeson ganinsa yayi zan kirasa yakuwa amince yanajin dadi, Yadauka wani abune kwarton maryam yana zuwa, Da kamar awa daya nakira Abdul azeez nace yazo da sauri kuma kar yazo da motarsa………… Kukasance tare dani a AURE KO ZAMAN GIDA part AURE KO ZAMAN GIDA *PART 13 Na Hauwa M Jabo. Tunda muka iso nake tunanin yanda zan bullowa plane in mishi magana amma nakasa saboda banga fuskaba sai nayanke shawarar bari in toneshi ingani haushi zaiji idan yaji haushi sai inbashi haquri haka kuwa akayi bayan sallar isha yana zaune kamar wani gunki nazo ina kur6ar tea ahankali nace masa kana tunani uwar yayanka maryam ne...!??? Ya waigo ya kalleni cike da mamaki da al'ajabi nasake maimaita abinda nace naqara da cewa ko in samo maka pic dintane ka kalla ko kaji sanyi,? Namiqe tsaye nace ko kawai kabita qiyama ku soye acan zaifi kazo nan kana tunaninta ko ka kar6o yaronka agurin kwarton matarka nasan shi yake damunka.!, Na kama hanyar dakina naji an kamoni ta baya da qarfi wllhy jabo saida cup din da yake hannuna ya fadi, Kinsanni akwai iskanci amma akwai tsoro, Ya jawoni daf dashi ya d'ago kaina da qarfi yana kallona har inajin nunfashinsa yana dukan fuskata yace wllhy wllhy Wllhy..!!! Idan kika qara yimin maganar maryam da mustafa sai kingane baki da wayo a gidannan ya dallamin wata muguwar harara sannan ya sakeni, Nace nasan zaka iya kasheni ma tunda na rabaka da uwar yayanka da danka da kake tunanin ita kadai zata iya haifa maka yaya, A fusace na fadi maganar ashe mutumin yagane kishi nakeyi, Sai yayi murmushi kawai yaje yazauna, Nasha jinin jikina na wuce daki sumuy sumuy kamar munafuka, Bayan kamar awa uku sai gashi yashigo dakina naji tsoro sosai, Yazo daf dani yazauna ya sunkuyar dakanshi yacemin zaki'iya zama dani zainab.? Araina nace miya kawo wannan tambayar? Kinyi shiru ina tambayarki zaki iya zama dani ko yaya?? Nanma ba amsa ba, Ya d'ago kai ya dubeni yace, Zainab arayuwarki na cutar dake fiye da tunanin duk wani makhluqi, Zainab banta6a son wata ya maceba sai akanki, Tun kina yar shekara tara na nemi mahaifinki ya bani aurenki kuma ya amince inda na fara ganinki kinje wani gida kina talla sai wasu yara suka qwace miki cinikin da kikayi duka suka gudu kina kuka na hadu dake natambayeki kikamin bayanin yanda akayi na biya kudin nakuma rakaki har qofar gidanku idan zaki iya tunawa, Wllhy tun lokacin Allah ya dasamin sonki azuciyana nagayawa babanki yace yamun alqawari zai bani ke da yake lokacin ina boarding school nakoma makaranta duk abokaina sun san sunanki har naqare karatu naje university ina university Kullum sai inzo da mota inyi parking inda kuke tsayawa talla inyi ta kallonki har ki saida waranki har nazo nafara sayen waran ina cewa kiyi sadaka amma darana daya baki ganni ba bakiga fuskataba lokacinda naga kinfara tasawa nayi tsoron kar wani ya kwaceminke nayi magana da iyayena dagyar suka amince kuma nagayamusu yanda nashirya za'a dauramin aure dakene dan kar wani ya gwacemin ke nacewa babanki ki riqa saka hijab hadda niqab kuma duk suka amince da hakan akan zanje wani..... Kukasance tare dani a AURE KO ZAMAN GIDA part 14 AURE KO ZAMAN GIDA 14 Na Hauwa M. Jabo …Course idan nadawo saiki tare Kullum kina raina amma nayiwa iyayena alqawarin saina qare karatu zanyi maganarki, A iran na hadu da maryam maryam tanunamin qauna ta gaskiya tun kafin muyi aure muke harka da ita kuma banta6a ganinta da alamar cewa tanada saurayiba nandanan nayi maganar aurenta ba musu aka amince dan dad dinta abokin dad dinane sosai, Ban ta6a son maryam ba saidai sha'awar ta da nakeyi saboda ta iya duk wata kissa da mace zatayi taja hankalin namiji matuqar yanada lafiya, Tanada abubuwan da nakeso ajikin mace wato nonuwa Kullum su suke rudani ajikin maryam sam ba ita nakesoba, Ta haifi Mustafa Allah ya dauramin son yaronnan har nake ganin idan bashi bazan iya rayuwa ba inason mustafa sosai lokackin nasami kaina kamar baniba, Sam ban damu dakeba sam ban damu da inji labarinkiba kullum daga maryam sai yaronta mustafa nima ina mamakin kaina sosai da yanda na cutar dake bayan aurenki na auri maryam amma maryam bata qaunarki mustafa yayi wani ciwo aka kaishi asibiti Dr yace damuwar mahaifiyarsa ce ta shafeshi kuma idan bamuyi hankaliba zan iya rasa mustafa nan dana hankalina ya tashi na rude ina tambayarta miyake damunta nan tace ita sai na sakeke nagaya mata bazan iyaba dataga ba nasara sai tace in mata alqawarin bazan kula dakeba matsawar tana da rayuwa Wannan ne na amince dashi dan gudun 6acin ranta ya shafi mustafa nadaina kulaki. Tun daganan nadaina kulaki duk dan mustafa yasamu lafiya amma ina shan azabar rashinki sosai sai gashi wacce na cutar na wulaqanta itace tazo ta fitarda rayuwata daga hadari ta ceceni zainab kiyafeni pls wllhy nayi danasanin abinda na aikata muki Kullum damuwar hakan ke sakani damuwa inasonki sosai zainab amma na cutar dake ya fashe da kuka mai ban tausayi wllhy hauwa jabo bansan lokacinda na rungumeshi ba ta baya ina rarrashinsaba lokacin na gama wayewa duk wani makirci na mata na iyashi duk a tv na iyasu wani channel (muharati zandagi) Rayuwar aurecekawai da zama da iyayen miji ake koyarwa, Duk wani rarrashin miji da tsokano mishi sha'awa na iyasu a lokacin, Na juyo dashi na lashe masa hawayensa na daura hannuna akansa cike da mur mushi nace masa duk abinda kamun na yafemaka nima ka yafemin tun daga ranar muka shirya da abudl azeez, Kinji tarihin rayuwata hauwa jabo, Hmmmmmmmm.. Kinyi mantuwa zainab bamu qareba baki gayamin first night dinki ba, hahaha ke hauwa jabo miye naki aciki tarihinane kuma na baki, Kiyi haquri ki qarasa min kinsan zee khalifa idan na bata labarin bawannan bayanin bazataji dadinsaba, Dan nasan tafison nan da ko ina, hahahaha, Owk zan fadamiki ne saboda namesake dina amma bari muyi sallah ko jabo...? Kukasance tare dani a AURE KO ZAMAN GIDA part 15 ♥♥♥AURE KO ZAMAN GIDA 15 Na Hauwa M. Jabo …Bayan mun qare sallah mukaci abinci taci gaba da bani labari, Ingayamiki jabo ranar tare muka kwana da abdul amma ba abinda yamun, Mun kwana biyu da shiryawa ranar na uku ina bacci sai na farka ashe mutumin naki idonsa biyuu daganandai aka raya sunnai Tun taga ranar muka shirya da mijina sai Kinga yanda muke rayuwa dashi gwanin ban shi'awa yana bani muhimmanci fiye da tunaninki jabo, Duk wata al'ada ta Iranian ita yake mun dan kuwa duk inda zamuje shi yake daukarmin jaka shi yake daukan beby kuma yana riqe da hannuna, Wllhy hauwa jabo nikaina banason yanda yakemun kinga nan Nigeria idan akaga mijinki yana miki hidima sai ace kin mallakeshi yazama mijin hajiya alhalin ba haka bane so da soyayyah ne ya haifar da haka, To ina kika iya Turkish?? Kai hauwa jabo akwai son labari to honeymoon mukajeyi Turkey achan na iya tukish, Gaskiya labarinki yamun dadi sosai zainb, Muna zaune sai ga mijin yashigo inaga baisan cewa akwai baqi agidanba taje da gudu ta rungumeshi yafara kissing din bakinta ina kallo hannunsa na murza basawanta ahankali bashiri nayi gyaran murya, Sai yasauke hannunsa akan basawanta ya juyo yace baquwa mukayi nace eh sannu dai jabo nace yauwa, Zainab tace nabata labarin wahallada ka banine kaida uwar yayanka taga ya lumshe ido yace yazanyi son maryam dina ya rufemin ido banaji bana gani sai ita a really miss u my mery.!! Tuni naga ta chanza fuska na tabbatarda kishine yake damunta tajuya zata tafi yabi banyanta da gudu yana dariya nakai 30mnt ni hauwa jabo ina jiran sufito amma shiru sun mayar dani kwalin taba nadauki yar wayata naqara gaba amma naji haushi sun manta dani Lallai yau naga aya, Inama ace nice.. Laifin dadi qarewa Hauwa Muhammad jabo take muku sai wata rana sai mun hadu a sabon littafi mai suna qarin jini, adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *