
Bakin Kishi 1
Posted by ANaM Dorayi on 08:16 AM, 29-May-15
Farko
Ta sunkuyar da kanta da sauri kana ta sa tafukan
hannunta ta rufe idanunta, "Allah da gaske ka ke
Alhaji?". Ta bukata da muryar kunya.
"Allah da gaske na ke Zainab...Ni fa mallakar ki
ce kawai hutu da kwanciyar hankalina a yanzu.
Wai ki na tunanin idan ban mallake ki ba, zan iya
ci gaba da kyakkyawar rayuwa? Kin ko yarda da
son da nake miki?"
Ta yi gaggawar girgiza kai, "Wallahi ba haka ba
ne Alhaji." Ta fada da saurin baki, a lokaci guda
kuma ta na mai ci gaba da girgiza kan. "Wallahi
Alhaji na san ka na so na, kuma na yarda da
sonka gare ni, kamar yadda na ke fada maka
kullum ne, abu guda kawai na ke jin tsoro a
tattare da aurenka...".
"Dakata Zainab". Ya katse ta ya na mai daga ma
ta hannu, "Ni fa sam-sam ba na kaunar ki rika
dawo da hannun agogo baya. Ya kamata zuwa
yanzu a ce kin gamsu da abubuwan da na jima
da fada miki. Don Allah ki saki ranki, ki manta da
wannan...shin wai akwai wanda ya isa ya hana
ikon Allah yiwu wa? Ko kuma idan Allah ya
tabbatar da ke a matsayin matata duk dunutar
nan akwai wanda ya isa ya hana? Wannan abu
da ba kanta farau ba." Ya yi kasa-kasa da murya,
"Don Allah ki sa tsintsiya ki share wannan daga
ranki...komai na Allah ne".
"Haka ne". Zainab ta ce da nisawa, "To Allah ya
taimake mu, Ya zaba mana abin da ya fi alkhairi
gare mu."
"Amin". Alhaji ya amsa a takaice, kana ya ce,
"Amma fa addu'arki ba ta cika ba."
Ta daga kai ta dube shi fuskarta kunshe da
alamar tambaya.
"Mene ne saura a cikin addu'ata?" Ta bukata.
"Sai kin biya zan fada miki." Cewar Alhaji.
"Nawa ka ke so a ba ka?" Ta ce da dariya.
Ya nuna ta dan yatsa, "Zainab na ke so a ba ni".
Ta yi dariya bayan ta sunkuyar da kai, "Ai dama
Zainab taka ce, tunda babu wani a zuciyarta sai
Alhaji Basiru. Nemi wani abin daban, wannan ka
samu."
ya yi dariya, "To ai shi kenan...dama ni Zainab ce
burina, tunda kuwa tawa ce ai shi kenan an biya
ni. A cikin addu'arki kin manta ba ki ce Allah ya
kara mana dankon soyayya da kaunar juna ba."
Ta kasa dago kai ta dube shi don kunya, "Ai
wannan addu'a ita ce a ruhina Zainab kowace
rana, a kwance, a zaune, a tsaye ko a tafiye,
babu
abin da Zainab ke yi sama da wannan addu'ar".
Ya ji dadin abin da ta ce don haka sai da ya yi
wata yar takaitacciyar dariya kafin ya ce, "Na
gode kwarai zainab, kuma ina yi wa Zuciyarki
albishir da cewa, ni ma haka na ke, kowace rana,
ko yaushe, a cikin kowane lokaci da ke na ke
motsi a cikin zuciyata. Babbam fata nashi ne,
Allah ya tabbatar da kyakkyawan kudirinmu, a
wayi gari a zahiri kin zama mallakata, ba a bafini
ba."
"Amin". Ta amsa a zuci. A zahiri kuma
murmushin jin dadi kawai ta yi.
"Ya na ji kin yi shiru ba ki ce komai ba?" Ya ce
ya na yi ma ta wani irin kallo.
"Na fada fa a zuciyata." Ta ce har lokacin kanta
a duke.
"To ai ni ban ji ba".
"Yanzu ya ya ka ke so a yi?" Ta bukata.
"Ina so Zainab ta dago kanta, ta kalle ni ta kuma
amsa mini da, amin". Ya ce idanunsa a kanta.
Ta dago ta kalle shi. Da sauri sai ta kuma mayar
da kanta ta dukar, "Ni ba zan iya kallon ka na
fada ba."
"To ya ki ke so a yi?" Ya bukata.
"A yafe mini na fada a haka." Ta ce da muryar
kunya.
Ya yi murmushi, "An yafe, fada a hakan".
"Amin". Ta fada da wata irin tattausar murya.
"Amin me?" Ya dawo da hannun agogo baya.
"Amin, Allah ya kara mana kaunar junanmu ko?"
Ta ce da karfin hali.
"Au tambaya ma ki ke?"
Ta girgiza kai da sauri.
Su ka fashe da dariya lokaci guda.
***
Alhaji Basiru ya yi murmushi a karo na farko tun
tsawon kusan mintuna talatin da su ka shafe su
na musayar yawu da maidakinsa Hajiya Rukayya.
"Ba ki fahimce ni ba Hajiya... Wallahi a cikin
wannan al'amari ba na nufin tozarci ko cin zarafi
a gare ki, kuma ko da wasa ba..."
Dole ka ce haka." ta katse shi murya na rawa,
"Dole ka ce ban fahimce ka ba Alhaji...ya za a yi
ka fahimta na fahimta, ai abin sai ya yi yawa?"
Ta tsahirta ta na kokarin daidaita numfashinta da
ke ynkurin dauke wa. Hakan shi ya haifar da
shirun wucin gadi a tangamemen falon.
Yau kusan watanni biyu kenan da Alhaji Basiru ya
fara fuskantar wannan matsala a wajen
uwargidan tasa. Koda ya ke ba ya raba daya biyu
ya san dalilin da ya jawo hakan, bai wuce
shawartar ta da ya yi ba akan zai kara aure.
A kalla shekarunsu uku su na zaune, zama na
lafiya da kwanciyar hankali, har da arzikin yaya
biyu mata (yan tagwaye), amma tun da ya
shawarce ta kan karin auren, kwanciyar hankali
ta karanta a gare su.
Alhaji Basiru ya numfasa bayan dan gajeren
tunani da ya yi. Kamar koda yaushe kokarinsa
daya ne, duk lokacin da su ka yi irin wannan
sa'insa, ya gamsar da ita ta amince da halaccin
kara auren nasa.
Da sanyin murya ya soma da kiran sunanta.
Ba ta ko daga kai ta kalle shi ba balle ta amsa.
Hakan bai dame shi ba. Ya ci gaba, "Gaskiya ban
taba tsammanin za ki bijire wa wannan abu da
na
zo miki da shi ba, musamman ma da na yi
la'akari da cewa, addinin musulunci ne ya ba ni
damar yin wannan abu, kin kuwa san shi kadai
ne
addini a wajen mahaliccinmu. Kada fa ki manta
Allah madaukakin sarki, a cikin
Alkur'ni mai girma cewa ya yi, "Ku auri bibbiyu,
uku-uku, hurhudu, idan ba za ku iya adalci ba ku
auri daya..." To kin ga anan ina da kwakkwarar
hujja ta kara aure, tunda kuwa insha Allahu zan
iya yin adalci a tsakanin..."
"Ka ga saurara Alhaji". Ta kuma katse shi a karo
na biyu, sai dai wannan lokacin cikin karaji ta yi
maganar, kuma muryarta na kunshe da alamun
tsiwa sabanin maganganun da ta yi a baya.
Lokaci guda kuma ta mike daga kan tattausar
kujerar alfarmar da ke cikin jerin kujerun da su
ka
gewaye falon.
Da muryar tsiwa ta ci gaba da cewa, "Dole ka yi
min wa'azi yanzu tunda ka na bukatar aure, Na-
mamajo! Ai a lokacin da ka ke matsiyacinka
tsumma gaba tsumma baya ba ka tarka ba, sai
yanzu da mu ka gama shan wahalarmu, ka ga ka
yi arziki za ka je ka auro wata banzar-bazara
wadda ba ta san halin da mu ka shiga ba, ta zo
ta ci bulus! To, ba zai yiwu ba, wallahi ba zai
taba yiwu wa ba, ka ma sake tunani tun dare bai
yi ma ka ba...domin kuwa na sha alwashin
matukar ina motsi a doron kasa kuma ina cikin
gidan nan, babu yadda za a yi wata shashasha ta
zo ta samu gindin zama balle har ta mike kafa".
Ta tsahirta ta na duban sa, duba mai cike da
raini.
Na-mamajo. Ita ce kalmar da ta fi sauran bata
wa Alhaji Basiru rai a duk tarin masifar da ta yi
masa, domin ya san mayen mata, shi ne abin da
kalmar ke nufi.
Sai dai kuma duk da hakan, ko kusa ko alama ba
zai iya yi ma ta komai ba koda ran nasa zai
tafasa ya kone ne saboda abin da ta yi masa,
don kuwa shi dai Allah ya jarrabe shi da tsananin
son ta, ga shi ya ki jinin rabuwa da ita. Aure dai
zai kara ne saboda umarnin Mahalicci da kuma
son da ya ji ya na yi wa wadda zai auro.
Amma a nata bangaren ba ta la'akari da hakan,
shi ya sa duk kalmar da ta fado bakinta ba
ruwanta da ta tauna kawai za ta yaba ma sa ita,
ita kuma a tunanin ta hakan ne kadai zai sa ta yi
nasarar dakushe yunkurinsa na kara auren.
Sai dai abin da ba ta sani ba shi ne, duk da irin
son da ya ke ma ta, ya kuduri aniyar babu abin
da zai hana shi kara auren ko ana ha-maza-ha-
mata.
Ya numfasa da karfi bayan tsawon lokaci da ya
dauka ya na tunanin irin soyayyar da su ka tafka
da matar tasa kafin wannan lokacin. Ita kuwa ta
na tsaye a kansa kerere kamar falwaya.
"Ki kwantar da hankalinki Hajiya". Ya ce bayan ya
daga kai ya dube ta, "Zauna, na ga har zuwa
yanzu ba ki gamsu da..." sauran maganar ta
makale a fatar bakinsa ganin ta juya ta nufi kofar
da za ta fitar da ita daga falon. Ya bi ta da kallo
cikin damuwa kamar mai kirga takun sahunta har
ta fice daga falon.
***
Kamar kowace safiya, yau ma ita kadai ce zaune
cikin dakin nata, ta yi tagumi ta na sake-saken
hanyar da za ta bi don ganin bayan kishiyar tata,
abin da ya zame ma ta wajibi a kowace safiya
tsawon shekaru ukun da amaryar mijin nata ta
tare. Fadi-tashi, kujiba-kujiba da buge-buge babu
irin wanda ba ta yi ba don hana auren amma
abin
ya faskara, aka zo aka yi auren, yanzu kuma ga
amaryar kullum kara samun gindin zama ta ke yi
a gidan.
Sau da yawa takaici da bakin ciki su kan lullubeta
ta idan ta tuna da rashin goyon bayan da
mahaifinta ya nuna tun farkon al'amarin, sa'ar
da
ta je ma sa da batun za a yi ma ta kishiya.
"Kada ki kuskura na sake ganin kafarki a gidan
nan matukar akan wannan maganar ce,
mutuniyar banza. Idan kuwa ki ka ki zan saba
miki". Maganar da mahaifinta ya gaya mata akan
lamarin ta bijiro ma ta a zuciya, ta ji kamar an
harbo wani mashin bakin ciki ne ya soki zuciyar.
Duk da dai a wancan lokacin mahaifiyarta ta yi
wa mahaifin nata martani da cewa,
"Haba Malam, gaskiya bai kamata ka ki goyon
bayan yarka ba akan wata can".
A fage guda kuma, alwashi da alkawarin da ta
sha dauka na ba wadda za ta shigo gidan muddin
ta na raye, shi ya ke dada daga mata hankali.
"Lallai ya dace na dauki matakin gaggawa akan
yar iskar nan". Ta tsinci kanta tana mai fada a
fili, wanda kuma shi ne abin da ta saba duk
lokacin da ta yi irin wannan tunani.
"Tabbas lokaci ya yi da ya kamata na san duk
yadda zan yi na ga babu ita a gidan nan, ko don
na cika alkawa..." Sallamar da aka yi a bakin
kofar dakin ta katse furucin nata.
"A'a, ah! Baraka...yaushe a gari in ji maki bako.
Saukar yaushe? Ta ce cikin fara'a bayan ta kawar
da alamun tunani da damuwar da ke kan
fuskarta,
sannan da gaggawa ta mike ta tari yar siriyar
matar da ke kokarin shigo wa dakin.
"Oh! Hajiya Rukayya ashe rai zai ga rai". Siririyar
matar da ke amsa sunan Baraka ta ce ta na
duban tsarin dakin cikin mamaki.
Hakika ta san cewa shekaru da dama da su ka
wuce dakin ba haka ya ke ba, duk abubuwan da
ta sani na daga cikin abin da aka kawo wa kawar
tata a sa'ar da ta na amarya babu a ciki yanzu.
Kai idan banda ta na tsoron kada ta yi karya ma
da sai ta ce hatta kusoshin da aka kafe labulen
dakin ba wandada su ka kawo Hajiya Rukayya da
su ba ne.
Koda ya ke tunanin nata bai zurfafa ba, da ta
tuna da labarin shaharar da aka ce mijin nata ya
yi.Yau rabonta da su hadu da Hajiya Rukayya tun
ranar da ta tare a gidan mijin nata lokacin ya na
talakansa. Tun daga wannan rana ba su sake
haduwa ba, sai a yanzu saboda tashin da su
Barakar su ka yi su ka koma jihar jigawa.
"Wayyo Allah makashin kakana". Baraka ta ce
daidai lokacin da ta zauna a daya daga cikin
manya-manyan kujerun laushin da ke cikin dakin.
Hajiya Rukayya da Baraka su ka gaisa cikin fara'a
da murnar haduwa da juna.
"Cewa na yi bari na zo na gaida ke tunda ke
Allah
ya yi miki arziki kin manta da mu". Baraka ta ce
ta nayatsine fuska.
"Uhm! Ke dai bari". Hajiya Rukayya ta ce ta
naduban Baraka ido cikin ido. "Ba wani batun
arziki, gari ne kawai ya dagule mana...ke dai bari
na kawo miki ruwa ki tsotsa". Ta mike ta nufi
wata karamar na'urar sanyaya ruwa da ke
durkushe can gefe guda.
Baraka ta bi ta da harara. "Ban gane gari ya
dagule mu ku ba? Mutumin da ke cikin daula irin
wannan ya ce gari ya dagule masa? To, mu kuma
mu ce me?" Ta daga kanta zuwa saman dakin ta
naduban kyakkyawar fanka ruwan zuma da ke
makale ta nata faman aiki abin ta.
Hajiya Rukayya ta yi wani motsattsen murmushi
lokacin da ta dawo gare ta dauke da kwalin
tataccen lemon zaki hade da karamin kofi, "Fara
jika makogoron..."
"Ina fa zan iya jika makogorona ban ji cikakken
abin da ke damun aminiyar ba." Baraka ta katse
ta bayan ta dawo da dubanta gare ta, "Hajiya
wanda ke cikin daula irin ku jin irin wadannan
kalamai ai ba karamin tashin hankali ba ne..."
"Uhm! Ke dai bari Baraka." Hajiya Rukayya ta
shiga cewa bayan ta koma wajenta ta zauna,
"Wadannan kyale-kyalen ba su ne ba, al'amarin
ya fi karfin su Ni yanzu duk a banza na ke ganin
su...ke ni Wallahi da zaman su cikin halin da na
ke ciki, gwanda zamana cikin halin da mu ke ciki
farkon aurena da Alhaji".
Baraka ta yi tagumi hannu bibbiyu bayan ta
mayar da hankalinta sosai ga Hajiya Rukayya,
"To, ni ban gane abin da ki ke nufi ba. Yanzu ki
na nufin ki ce mijinki ba ya iya gamsar da ke ne
ko ya ya?" Ta yi shiru cikin saurare da mamaki.
"Duk ba haka zancen ya ke ba Baraka, na ga har
zuwa yanzu ba ki fahimta ba. Ba ki da labarin an
yi mini kishiya?"
"Laa....ila...ha...illallahu".Baraka ta yi doguwar
hailala ta natafa hannu, "Kishiya? Kishiya fa ki ka
ce? A garin ya ya haka ta faru?"
"Ke dai bari Baraka, Kishiya na gaya mi ki har da
danta daya yanzu a gidan nan". Hajiya Rukayya
ta fada ta na gyara daurin dankwalinta, ganin ta
gamu da irin mutanen da ta ke son gamu wa da
su (Wadanda za su taya ta alhini da nuna rashin
jin dadinsu ga halin da ta ke ciki).
"Ba shakka!" Baraka ta ce ta nagyada kai, "Ke
kuma ki na zaune ki na kallo?"
Ta yi shiru bayan ta dubi kasa, "To ya ya na iya
da wannan shegen naci na Alhaji". Ta ce ta
natabe baki. "Ba ki ga irin wutar da na hura
masa
ba kafin a yi auren, amma da ya ke Na-mamajo
ne duk a banza, sai ya mayar da komai ba komai
ba...".
"To na ji, yanzu wane mataki ki ka dauka? Ko ki
na nufin an fi karfin ki?" Baraka ta katse ta.
Hajiya Rukayya ta numfasa, "To, kusan haka din
ne Baraka, kin san al'amarin ne..."
"Kin ga saurara!" Baraka ta sake katse ta, "Ba
wani al'amarin, kawai sakacin ki ne...kya hura
masa wutar murhu ki ce kin hura masa wuta? Ai
wutar gidan burodi za ki hura masa ki gani idan
zai kai labari. Bayan haka ga hanyoyi nan burjuk
da za ki dauki mataki kin tsaya ki na cewa
al'amarin ne... To tsaya ki na fadin al'amarin ne
har ta kuma haihuwar wani da namijin, kin ga shi
kenan kin fi ta shan wuyar miji, ita kuma ta fi ki
more shi, tunda ke duk yayanki mata ne, kinko
san a gado duk namiji daya rabon mata biyu gare
shi. Wannan ai shi ne kura da shan bugu, Gardi
da karbar kudi. Idan da ni ce ke da tuni ba a yi
an gama da shegiya ba...duk malaman garin
nan?"
"Uhm!" Baraka kenan". Hajiya Rukayya ta fada da
nisawa, "ke ce ki ke ganin a zaune na ke, ban da
tsananin azaba da masifa da na ke yi mata da
baki na, amma kin gan ta nan shegiya, zama
daram a gidan nan sai ka ce ba ita na ke yi wa
ba."
Baraka ta saki wani dan murmushi iya fatar baki,
"Wannan magana taki da ban mamaki ta ke...wai
kin bi duk malaman garin nan. Uhm! Kin dai bi
iya
wadanda ki ka sani. To, wai tsaya, mahaifanki ba
sa taimaka miki?"
Hajiya Rukayya ta yi dariyar takaici "Ke ma dai da
bata bakinki ki ke, sanin kanki ne ba zan samu
goyon bayan Baba ba, ga shi kuma shi ne
tsayayye akan gidan. Kin san shi irin mutanen
nan ne ma su halin mutan da, bai damu da abin
duniya ba. Babu yadda Umma ba ta yi ba wajen
ganar da shi, amma daga karshe ba ki ga fadan
da ya yi min ba lokacin da na matsa akan abin,
kamar ya hada mu ni da Umma ya daka, wai shi
ba mutumin banza ba ne."
Baraka ta jinjina kai kana ta yi shiru na dan
lokaci, "Lallai ki na cikin wahala Rukayya idan har
ki ka biyo halin mahaifin nan naki, Wallahi ba
abin da za ki tsinana, sai ki zo duniya a banza ki
koma a wofi" Ta tsagaita ya naduban Hajiya
Rukayya, jin ba ta da shirin cewa wani abu ya sa
ta ci gaba "Yanzu a ina ki ka tsaya, ko kuma
wacce shawarar ki ka yanke? Hajiya Rukayya ta
saki wani guntun murmushi na
jin dadin damuwar da Baraka ta nuna, kana ta
ce,
"Wannan shi ne abin da ki ka zo ki ka same ni
ina yi Baraka, kin san tun da ta shigo gidan nan
ban samu zama da sukuni ba, kullum kulle-kullen
ganin bayanta na ke yi." Ta rage amon muryarta
kamar mai tunanin wani zai iya jin abin da za ta
fada, "Ni fa yanzu kuma na fi tsanar dan nan
nata
saboda abin da ki ka hango mini na game da
gado don dai kawai ban san yadda zan yi na
kawar da shi ba ne..."
"Ba ki dai nemi shawara ba." Baraka ta katse ta,
"Ai da kin nemi shawara da tuni kin gama da su
ma duka ba shi kadai ba. Nawa su ke Allah na
tuba?"
"To, a wajen wa ki ke tsamanin zan sami
sawarar?"
"Hajiya Rukayya ta ce a marairaice, "Dama ke
kadai ce abokiyar shawarar tawa tun muna yara,
sai kuma furera, ita kuma yanzu babu Naira a
gabanta, idan na kai mata wannan shawarar
cewa za ta yi na bi duniya a sannu, duniya ba
wajen zama ba ce. Kin riga kin san halinta dai
tun a makaranta, mutuniyar da ko Alli ka dauka a
lokacin za ta fara maka wa'azi Allah ya ce,
Annabi ya ce. Wannan dalili ya sa na rufe kofar
shawara da kowa na ke gaban kaina, ke kuma kin
yi nisa da mu."
Baraka ta yi jigum ta na sauraron ta kamar mai
tunanin wani abin kirki har Hajiya Rukayya ta
tsahirta. Ta nisa, "To kin ga kwantar da
hankalinki yau dai zance ya kare tunda na
zo...wa ta ke da suna kishiyar taki?"
"Zainab". Hajiya Rukayya ta fada da saurin baki.
"To, ina so ki ji a ranki Tuni Zainab ta bar gidan
nan."
Baraka ta ce ta na zare idanu.
"Me ya sa ki ka ce haka?" Hajiya Rukayya ta
tambaya.
Ta yi wani kwakkwaran numfashi kana ta ce, "Ina
da wani mutum ne sha yanzu magani yanzu,
aikinsa kamar yankan wuka ya ke. Saboda haka
idan kin shirya, ki na da wasu yan kudade a kasa,
ki zo kawai mu je ki ga aiki da cikawa."
Hajiya Rukayya ta nisa cikin mamaki. A tunaninta
yadda ta sha wahalar bin malamai kamar ba za a
samu wani wanda zai iya biya mata bukatarta
ba.
"Kar ki yi shakka kwalliya...wallahi wannan
mutumin da zan kai ki wajensa ba dama ne"
Baraka ta ce ganin ta yi shiru cikin tunani.
"Allah Ta-hannun damar". Hajiya Rukayya ta ce
bayan ta dan saki ranta.
"Au! Ke naki ma wasa ne. Ai idan kin shirya kuma
akwai kudi kamar yadda na fada miki, an yi an
gama jinyar mayya. Saboda kwarewarsa fa har
kirari ake masa da Mai-gobe-da-nisa. Tab! Ai
wannan ya yi nisa, ya ci dubu sai ceto."
Hajiya Rukayya ta kuma nisawa cikin jin dadi,
"yanzu ki na nufin za a samu biyan bukata idan
an je?" Ta kuma jinjina abin.
Baraka ta dan bata rai, "Don Allah kar ki sa raina
ya baci, ni ce fa na fada miki. Ko ba ki yarda da
ni ba ne?"
Har yanzu akwai kokwanto a fuskarta saboda
tunanin irin wahalar da ta sha, amma ba ta
samu
biyan bukata. Amma don ganin ran Baraka ya
soma baci sai ta yi ta maza ta saduda, ta mika
wuya, "Yanzu ke ce abar ji, Akuyar daure, mara
yanci."
"Kin ci abinci Baraka." hajiya Rukayya ta ce ta
nadariya, "kuma kar ki damu, ni ma na kusa
samun yanci tunda yanzu na hau hanya, kin san
kuwa sannu ba ta hana zuwa...saboda haka ki sa
mana rana kawai, babu wani abu."
Baraka ta cira kai ta naduban kyakkyawan rufin
dakin da aka yi matukar kawata shi, alamun ta
na tunani, "Me zai hana mu je gobe idan ki na da
hali, tunda ni jibi zan koma."
Ba ta yi tunanin komai ba ta amsa, "Allah ya kai
mu goben lafiya. Amma fa kin san ba na son a
fara ta kanta, na fi son a fara ta kan wannan
shegen dan, musamman ma illar rayuwarsa da ki
ka fito mini da ita."
"Wannan kuma ya rage naki sabuwar amarya a
dakin miji...gobe idan mun je kya ma sa bayani.
Ni zan koma." Ta mike tsaye a hankali.
"Tun yanzu?" Hajiya Rukayya ta ce da ita cikin
daga murya.
"Wallahi akwai gurare da dama da na ke so na
kai ziyara kafin na koma jibin, sai dai goben
kawai kya ganni."
"To, Allah ya nuna mana" Hajiya Rukayya ta ce
bayan ita ma ta mike tsaye, "Mu je na taka miki."
To, a daidai lokacin ne Zainab ta daga labulen
dakin ta shigo gami da sallama, shigowar da ta
zamar mata da-na-sani.
"Wa'alaikis sa..."
Yunkurin amsawar da Baraka ta yi ya gaza kai
gaci saboda zungurarta da Hajiya Rukayya ta yi
gami da cewa, "Ke ita ce fa!"
Baraka ta fahimci wadda ta ke nufi, don haka sai
ta mayar da dubanta ga Zainab, a tsanake ta
shiga yi mata duban Raini da wulakaci, kamar
yadda ta ga Hajiya Rukayyar ta galla mata wata
uwar harara.
Ita kuwa a nata bangaren maimakon ta damu, sai
ta saki wani matsakaicin murmushi, "Yaya
bakuwa mu ka yi ne?"
"Bakuwa? Ina ruwanki da bakuwa? Ta ki ko
tawa? Haijaya Rukayya ta ce fuska a yatsine
kamar yakuwar da ta sha matsa.
Zainab ta yi kasake ta nakallon su cikin kunya.
"Da ke na ke! Bakuwarki ce ko tawa?" Ta kuma
fada da tsawa.
Zainab ta nisa kana ta kuma yin murmushin
karfin hali cikin son mayar da abin wasa ta ce,
"Tawa ce mana tunda ta ki..."
"Ke rufe mana baki sarkin iya magana, wa za ki
yi wa wayo." hajiya Rukayya ta kuma katse ta,
"Ki ji mu da yarinya?" Ta juya ga Baraka wadda
tunda al'marin ya fara babu abin da ta ke yi sai
hararar Zainab din, "A to! Ni ban ma san ta ba,
amma kin ji saboda
kalen dangi wani bakuwarta ce...ko ta ya ya na
zama bakuwarta?"
"Oho!" Cewar Hajiya Rukayya, "Wa ya san ma ta,
kin gan ta nan kullum haka ta ke shisshige mini
wai ita kanwa..."
"Kanwarki? A gidan uban wa?" Baraka ta katse
ta, "Dama an taba kanwa da abokiyar gaba?"
"Ke ma dai kya fada". Hajiya Rukayya ta fada
bayan ta mayar da dubanta ga Zainab wadda har
yanzu ke tsaye, kai sunkuye, cikin tsananin jin
kunya.
"Ke!" Ta daka mata tsawa, "Wai mene ne ya
kawo
ki daki na?"
Zainab ta cira kai a hankali ta dube ta, "Ba
komai, dama abinci ne na kammala na zo don na
sanar da ke".
"Abinci?" Baraka ta cafe ta naduban Hajiya
Rukayya,
"Abinci fa ta ce? Har abinci ki ke yarda ku ci
tare? Haba Gaskiya mana ki ka kasa fitar da ita
daga gidan. Ai ta riga ta cinye ki...kai lallai ma
Rukayya nan da wauta ki ke. Idan banda abinki,
wa ke cin abinci da kishiya, wadda idan aka ba ta
wuka aka ce ta yanka ki, a guje za ta aikata."
Hajiya Rukayya ta girgiza kai, a lokaci guda kuma
ta daga hannu, "Kin ga ni fa ba tare mu ke ci ba.
Ina ni ina cin abinci da wannan." Ta nuna Zainab,
"Ta dai gama ne, ta zo ta sanar da ni kawai. Yo
da na ci abinci da wannan ba gara na mutu da
yunwa ba."
Zainab ta dago kanta da ke duke da nufin ta ce
wani abu, sai baraka ta yi mata tsawa, "Ke
malama! Ba ma bukatar maganarki, maza-maza
ki fice ki ba mu waje tunda nan ba dakinki ba
ne."
Ba ta kuma wani yunkuri ba, ta juya jiki a
sanyaye, zuciyarta cike da nadamar shigowarta
dakin.
Hajiya Rukayya da Baraka su ka fashe da dariya
har da tafawa.
"Shegiya kadan ma ta gani." Baraka ta ce, "Yadda
na tilasta ma ta ta fita daga dakin nan, haka za
ta fita daga gidan nan ko da ba ta so."
Suka kuma kwashewa da dariya, kana su ka
rungume juna.
***
Wata dalleliyar mota kirar KIA picanto shudiya, ta
cusa kai cikin tafkekiyar harabar makeken gidan
bayan bude babbar kofar da maigadi ya yi.
Kai tsaye direban motar ya wuce da ita cikin
babbar rumfar kwanon da aka tanada
musamman
don ajiyar motoci, sannan cikin sauri ya fito ba
tare da ya kashe motar ba, ya bude kofar motar
ta baya.
Alhaji Basiru, baki, kakkaura mai matsakaicin
tsawo ya fito kallo daya za ka yi masa ka lakanci
ya na da fara'a sosai duk da wadatattun
kumatun
da ya ke da su.
"Sannu da zuwa Alhaji." Dattijo da ya bude mu su
kofa ne ya fada bayan ya isa gare su.
"Yauwa, sannu malam Bukar." Alhaji Basiru ya
amsa, kana kai tsaye ya nufi kayatacciyar kofar
da za ta sada shi da cikin gidan, zuciyarsa cike
da zulumin abin da zai tarar a gidan, wanda ya
zame masa sabo tun lokacin da ya kara aure.
Ya daga labulen babban falon shakatawar gami
da sallama.
Zainab kyakkyawar fara da ke zaune kan daya
daga cikin tausasan kujerun da ke kewaye da
falon ta amsa sallamar da tuni ta gane muryar da
ta yi ta. Cikin fara'a ta mike ta tare shi, ta karbi
karamar jakar da ke rike a hannunsa.
"Sannu da zuwa Alhaji." Ta ce.
"Yauwa, sannu amarya. Yau ke kadai ce a falon?
Ina yayar taki?" Ya amsa gami da tambaya.
"Ta na ciki wallahi, dazun nan ta shiga." Ta ba
shi amsa.
Ya nufi daya daga cikin kujerun ya zauna.
"Bari na kawo ma abin da za ka sanyaya
makoshinka maigida." Ta ce da fara'a bayan ta
ajiyr jakar a gefensa.
Cikin nutsuwa ta mike ta nufi doguwar na'urar
sanyaya ruwa da ke ajiye a can gefe guda, hakan
shi ya yi daidai da lokacin da Hajiya Rukayya ta
daga labulen falon ta shigo ba tare da sallama
ba.
"Sannu da zuwa." Ta ce da kyar kamar mai ciwon
baki.
"Yauwa. Sannu uwargida, kwanciya ki ka yi ne?"
Alhaji Basiru ya amsa tare da yi ma ta tambaya
cikin rashin damuwa da hade fuskar da ya ga ta
yi.
"Wane ne ya ce ma kwanciya na yi?" Tambayar
kenan da ta fito daga bakinta.
Alhaji Basiru ya yi murmushi, "Uwargida
kenan...mene ne na zafi cikin wannan tambayar?
Gani na yi idonki kamar da alamun barci."
Ta yi wani takaitaccen tsaki, "Ni ba barci na ke yi
ba, idan ma fada ma aka yi, wanda ya fada ya
zama babban makaryaci."
"To, ai shi kenan." Ya ce da ajiyar zuciya. Idan da
sabo dai ya saba. Wannan wata al'ada ce da ya
san ta dauka, ta mayar da karamar magana
babba, duk don kar a zauna lafiya.
Da yalwataccen murmushi ya dubi Zainab, wadda
ke kokarin darkusawa gabansa, hannunta na
dama rike da doguwar robar sassanyan tataccen
lemon zaki, karamin kofi rike a hannunta na
hagu.
"Yauwa, a gaishe ki amarya. Na gode." ya fada
bayan ya karba.
Ta mike cikin jin kunyar abin da ya fada, ta koma
kan kujerar da ke kusa da Hajiya Rukayya ta
zauna, sannan cikin sanyin murya ta ce, "Sannu
Hajiya, har kin fi..."
"Wane irin sannu...ciwo na ke yi?" ta katse
Zainab da daga marya, sannan ta shiga jifan ta
da wata uwar harara. Maganar ba ta yiwa Alhaji
Basiru dadi ba, don haka yace, "Haba Uwargida,
wai me ya sa ba..."
"Ka ga malam, babu ruwanka a cikin wannan
maganar." Shi ma ta katse shi, sannan ta ci gaba
da cewa "Ai dama kai ka ke
daure mata gindi, idan banda daurin gindin da ta
ke samu a wajenka, ya ma za a yi wannan yar
matsiyatan ta dora wa Hauwa'u sharri, wai ta
yaga ma ta littafi, alhali wannan dan banzan
yaron nata ne marar jin magana kamar barawo
ya yaga kuma ma wani rainin hankali, na yi
magana yarinyar nan ta rufe idanu ta yi min
rashin mutunci a gidan nan, zagi ta uwa ta
uba..kai in banda ruwa ya daki babban zakara,
wannan yarinya ta isa ta ja da manyan mata,
yarinyar da na tabbatar a haihuwar kaji na haife
ta sau babu iyaka.." Ta dan sarara kadan, sannan
ta ci gaba da cewa, "Ko da ya ke ba na mamaki
don shi matsiyaci idan ya samu dama babu abin
da ba zai iya.."
"Ke saurara Hajiya! Zainab ta katse ta cikin fushi
tuni fuskarta ta sauya. Da kaushin murya ta ci
gaba da cewa "Ina so fa ki sani duk abin da ki ke
mini kyale ki na ke yi saboda gudun ka ce-na ce
da kuma darajar wanda mu ke aure, amma ba
don tsoron ki ba. Kar ki ga ina kauda kaina akan
wasu abubuwa ki yi tsammanin ban san abin
da.."
"Zainab" Alhaji Basiru ya katse ta ta hanyar kiran
sunanta. Da girgiza kai ya ce, "kar na kara jin
bakinki"
Ranta ya yi mutukar baci, amma duk da haka sai
ta shiga tausasar zuciyarta don bin umarnin mijin
nata
Ita kuwa Hajiya Rukayya sai ta mike tsaye ta
natafa hannu ta nafadin "Ka kyale ta mana ta
gani idan da yau sai na dandaka ki a gidan nan,
don ina da tabbacin ko daga barci na tashi na fi
karfin ki." Da wannan maganganu ta fice daga
falon.
Bayan fitar ta sun dauki tsawon lokaci babu
wanda ya ce da wani komai.
Alhaji Basiru mamaki ne ke damun sa da
tunanin,
yaushe za a kawo karshen wannan abin da ke
faruwa a gidansa. Da ya ke ya san mai laifin sai
ya numfasa a hankali, ya dubi Zainab, "Ki kara
hakuri akan wanda ki ke yi da, komai na duniya
watarana tarihi ne." Haka ya ci gaba da tausar ta
saboda ko da yaushe dai kokarinsa ya daidaita
tsakaninsu, don ba ya son rabuwa da kowaccen
su, kamar yadda zuciyarsa ke ba shi shawara
wasu lokutan ya kawo karshen matsalar ta
hanyar saki. Amma idan ya tuna illar sa a
addinance sai ya danne zuciyar tasa ya lallashe
su.
Lokacin da ya tabbatar ya gama tausar zuciyar
zainab, sai ya mike ya bi bayan Hajiya Rukayya
da nufin ita ma ya tausashe ta don a samu
zaman lafiya. Amma ko da ya shiga dakin ya na
yi mata magana sai ta yi kamar ba da ita ya ke
ba. Don ya tabbatar ma ba za ta saurare shi ba
sai ta shiga rera wasu wakoki na habaici gare
shi.
A daidai lokacin da wannan ke faruwa, acan
bakin
kofar gidan ma wani abu ne ke faruwa tsakanin
malam Bukar maigadi da wasu bakin turawa da
su ka zo wajen Alhaji Basiru.
Turawan biyu yan asalin kasar Ingila ne, wanda a
nan fiye da rabin harkokin Alhaji Basirun su ke.
Kuma su ba sa jin Hausa, yayin da shi kuma
Malam Bukar ba ya jin Turanci.
Tsawon lokaci su ka kwashe suna musayar
yawun da ba shi da amfani, don kuwa babu
wanda ya fahimci dan uwansa, saboda rashin
gane abin da kowa ke cewa.
Baseer, shi ne abiin da turawan ke iya furtawa
na
daga sunan Alhaji Basiru.
"Na ce mu ku a nan gidan kaf Babu Baseer, sai
dai Alhaji Basiru kun ki yarda ko? To shi kenan
sai ku yi ta yi, idan kun gaji da tsayuwa kwa
tafi." Malam Bukar ya ce a kufule ganin suna
kokarin cusgunawa daddadan gyangyadin da su
ka zo su ka same shi ya na yi.
Turawan biyu su ka kuma duban junan su cikin
rashin fahimtar abin da ya ke nufi wanda kuma
shi ne abin da su ke yi duk sa'ar da ya yi
maganar.
"Have you understand what he is saying?" Daya
baturen ya ce da dayan.
Wanda aka tambaya ya girgiza kai, alamun bai
gane ba.
Baturen da ya yi tambayar ya kuma duban
malam Bukar fuska cike da alamun damuwa, ya
kuma maimaita bukatarsu gare shi.
"To, ai kuma sai ku yi tunda ni dai na yi mu ku
bayanin babu wani Baseer a nan kun ki yarda.
Yanzu kuma ga shi na ji ka tsiro da wani sabon
abu kamar ka na ambatar Talle ko mene ne? Sai
ku yi ta yi, dama ai mu na samun labarinku, ba
ku da aikin yi sai shariri ta..mutanen da ke kula
da lafiyar Beraye don sun tambayi abin da babu
har wani abin mamaki ne? Ya na gama gadar
haka ya rufe idanunsa kana ya langwabar da
kansa a kan majinginar kwantacciyar kujerar mai
kama da gado, wadda aka yi ta da icen makara
ya ci gaba da gyangyadi abinsa.
Turawan su ka kuma duban junansu cikin
damuwa kana su ka kuma kallon malam Bukar
wanda tuni ya fara layi irin na ma su gyangyadi.
Wanda ke yi ma sa tambayar ne ya tuno wata
dabara. A hankali ya mika hannu ya taba kafadar
malam Bukar.
Firgigit! Ya tashi sauran kiris ya hantsilo daga
kan kujerar. Daga bisani ransa ya kara baci da ya
ga cewa har yanzu turawan nan ne da ya tsana
da gani su ka tashe shi. Ya mike cikin fushi da
zummar kai duka gare su amma saboda labarin
da ya taba samu a kauyensu tun ya na saurayi
cewa, wai fararen fata jikinsu kamar nunanniyar
Gwanda ya ke saboda rashin kwari, idan baki ya
kuskura ya doke su mutuwa su ke yi domin wai
jini ne zai fito daga jikin nasu, su kuma ba sa
kaunar su ga jini a jikinsu, wai saboda haka sai yi
fushi su mutu. Tunanin hakan ne ya sa shi sauya
abin da ya yi
nufi a farko na kai mu su duka, zuwa fadin, "Kai
wai ku diyan gidan uban wane ne da za ku dame
ni? Na ce mu ku ba mu da wanda ku ke fadi a
gidan nan kun ki yarda. To, wai me ku ke nufi ne
don buhun ubanku?"
Turawan ba su damu da fadan nasa ba, don
dama ba sa jin abin da ya ke fada. Don haka
kawai sai dayan Baturen ya daga hannuwansa
biyu kamar yadda ya yi nufi, ya fara yi wa
malam
Bukar zance irin na kurame da su. To, a sannan
ne malam Bukar ya fara fahimtar su. Bayan dan
lokaci da ya dauka ya na duban Baturen sai ya
fahimce shi. Take shi ma ya sauya zuwa hakan.
Cikin kankanin lokaci su ka fahimci juna duk da
ba yarensu daya ba.
A cikin tattaunawar tasu ne, Malam Bukar ya
tambaye su, abin da ya sa ba su buga masa
waya ba.
Su ka sanar da shi sun nema ba su samu ba.
Da fara'a ya sanar da su, su yi jiransa ya je ya
sanar da Alhajin zuwan nasu.
***
Tabbas Malam Bahaushe ya yi kyakyawan tunani
da ya ce, " Sa kai ya fi bauta ciwo" Hakika haka
abin ya ke, don wannan karin maganar ya yi
tasiri akan Hajiya Rukayya wacce sau da yawa ta
kan gagara tashi sallar Asuba ko da kuwa an
tashe ta. Amma ga samun sauyi sai ga shi yau ta
tashi tun kafin kiran sallar farko, saboda bukatar
kanta.
Bayan ta yi sallar Asuba, a gurguje ta shiga
wanka, cikin mintinan da ba su fi a kirga da
yatsun hannu ba ta fito, kana a gaggauce ta
sanya kayanta ta fito fes da ita.
Ta isa ga wani tafkeken madubi da ke kafe a jikin
bango wanda a shi ne take yin kwalliya a duk
sa'ar da ta yi wanka.
Ta kare wa kanta kallo tsaf a cikin madubin kana
ta yi murmushi.
"To, yanzu me ya rage mini?" Ta tambayi kanta a
fili ta cikin madubin, kamar mai neman shawarar
siffarta da ta bayyana akan madubin.
"Abu uku ne kawai ya rage miki." Zuciyarta ta
kissima ma ta.
Ta fadada murmushinta lokacin da zuciyar tata ta
ci gaba da jero ma ta abubuwan da ya kamata ta
samu.
"Kudi da neman yardar Alhaji, da kuma jiran
zuwan Baraka" Yanzu su ne abubuwan da su ke
gabanta
Shakka babu ya zama dole ta nemi yardar Alhaji
Basiru a wannan karon, ba wai don ta nashayin
zai iya hana ta fita ba, a'a, saboda ta nason ta
fita da mota da kanta don gudun kar asirinta ya
tonu idan sun fita da direba.
Ta riga ta san duk abin da take so Alhaji Basiru
zai ba ta, ko don a zauna lafiya. Amma fa banda
barin ta ta ja mota. Haka dabi'arsa ta ke, ba ya
barin iyalansa su ja mota da kansu sai dai duk
inda za su a kai su. A tunaninsa, abin kunya ne a
ce mai kudi kamar sa ya bar matansa su na jan
mota da kansu. Tunda kuwa ta san da haka, lallai
akwai bukatar ta lallashe shi ta kowace irin
hanya don ya bar ta ta fita ba tare da direba ba.
Al'amarin kudi kuwa da sauki-sauki, don ta
natunanin wadanda ke hannunta ma za su iya
isar ta, duk da ya kamata ta nemi kari. Sai kuma
jiran Baraka, wanda ya zama dole don ita ce idon
garin.
Ta kuma yin murmushi cikin madubin a karo na
biyu, ta namai yabawa da kyakkyawan tunanin
da
ta yi.
A hankali ta juya, ta bawa mudubin baya kana ta
fara duban gefe da gefen dakin a tsanake kamar
mai tsammanin ganin wani a dakin bayan ita.
Ba wani abu ta ke tunani ba kawai ta na fasalta
adadin yan gaisuwa da zaman makokin da dakin
zai dauka ne.
Lokacin da ta isa dakin Alhaji Basiru a kishingide
ta same shi a kan doguwar kujerar da ke cikin
kujerun da ke dakin.
Sau biyu ta yi sallama amma bai dago ba balle
ya amsa. Ba wai bai ji sallamar ba ne, amsawar
ce kawai ta gagara saboda hankalinsa ya tafi
duniyar tunani, kuma ba wani abu ya ke tunani
ba
da ya wuce matsaloli na rigingimun da ke faruwa
a tsakanin iyalan nasa, da kuma hanyar da zai bi
ya warware su. Wannan shi ne tunaninsa a
kullum.
Sai dai baya ga wannan, yau akwai wani, tunanin
gayyatar da aka yi masa zuwa kasar ingila a
game da harkokin kasuwancinsa, wanda shi ne
dalilin zuwan turawan nan biyu wajen sa.
Abinda ya fi tunani a yanzu shi ne, ya ya iyalansa
za su kasance idan ya yi tafiyar da ya ke so ya yi
a jibi. Ya na nan ma ya aka kare?
Wannan shi ne ya sa a yanzu da Hajiya Rukayya
ta shigo cikin dakin ya gaza amsa ma ta sallamar
har sai da ta je kusa da shi ta dafa shi.
Ya cira kansa a hankali ya dube ta. Bai ce komai
ba ya kuma mayar da kan.
"Alhaji lafiya kuwa?" Ta tambaya da alamun
mamaki a fuskarta.
Ya nisa, kana ya kuma cira kai ya dube ta, "E, to,
lafiyar kenan." ya ce daidai lokacin da ya ke
yunkurin sauyawa daga kishingidar zuwa zama.
"Haba Alhaji, to mene ne abin yin dogon tunani
irin wannan bayan ka ce lafiya?" Ta ce bayan ta
samu waje ta zauna kusa da shi.
"Dogo ne tunanin nawa? Ya bukata ya na
sababben murmushinsa don gudun bacin ranta.
Don tun bayan karin aurensa, duk lokacin da za
su yi wata magana sai sun saba.
"Dogo ne mana..sau nawa na yi sallama ba ka
amsa ba?" Ta fada a marairaice.
Mamaki ne ya fi bayyana a fuskarsa fiye da
komai, don rabonsa da ya ji sassanyar muryarta
tun kafin ya tuntube ta da maganar karin
aurensa.
Ya kuma yin murmushi "Ina jin ki, kawai dai na.."
"Au! Ashe ka na ji na ma ka kyale ni? Ta katse shi
da tambaya ta naharararsa, harara
ta wasa.
"Ba haka na ke nufi ba, ki bari na karasa mana."
ya ce cikin murya mai cike da mamakin irin hirar
da ke gudana tsakaninsu. Ya kura ma ta idanu
cikin kokarinsa na gano wani abu tare da ita.
Ta dukar da kai kasa bayan ta fahimci abin da ya
ke nufi. A zahiri har a badini ba ta bukatar ya
gane yaudarar da ta ke kokarin shirya masa, don
ta samu damar fita da mota ba tare da direba
ba.
Sama da dakika talatin ba ta dago ba. Shi kuwa
bai daina kallon ta ba, zuciyarsa sai dawurwura
ta ke tsakanin yarda da rashin hakan, a dan abin
da ya nazarta a tare da ita.
"Ai kawai ka godewa Allah, da alama ya shirye ta
ne ta zo ta nemi afuwa ga abin da ta yi maka a
baya. Idan ba haka ba, me zai kawo ta dakinka
da sassafe kuma har ta rika yi maka magana a
tausashe?" Wani sashe na zuciyarsa ya ambata.
"Kai haba, ina! Ba wani nan, kai dai kawai akwai
wani abin daban." Wani sashen ya karyata na
farko.
To, ko ma mene ne dai a yanzu ya na bukatar ya
sani, kuma lokaci ya yi da ya kamata ya yi
amfani da wannan damar wajen shawo kanta don
su samu zaman lafiya da amaryarta.
"Hajiya ya na ga kin dukar da kai kasa kamar mai
dinkin hula?" ya bukata cikin raha.
"Dole na yi haka Alhaji tunda na zo takanas gare
ka ka ce ka na ji na ka kyale ni." Ta amsa ta na
duban sa, a wannan karon ta kara kwantar da
muryarta fiye da baya.
Ya kuma fadada murmushinsa na mamaki da jin
dadin ganin irin damuwar da ta ke nunawa, wai
don ya ce ya na jin sallamarta ya kyale. Take sai
ya ji kamar duk duniya babu wanda ya fi shi jin
dadi. Don a rayuwarsa babu abin da ya fi so irin
ya ga ya na zaune kalau da iyalansa.
"Ba ki fahimce ni ba. Cewa na yi na dan sha'afa
cikin tunani ne...amma ai ina jin ki."
"To, share ni ka yi kenan?" Ta sake bukata ta
nayi mai fari da idanu.
"A'a." ya ambata da sauri.
"To mene ne?" Ta ce ta nadariya, a wannan
karon sai da fararen hakoranta su ka bayyana a
fili, wanda hakan shi ma ya sa shi darawa.
"Yau kuma sai ina? Na ga kin yi kwalliya kamar
wata sabuwar amarya." Ya sauya hirar bayan sun
dakata da dariyar.
Ta harare shi, "Wa ya sani ko amaryarce?"
Ya yi mamakin abin da ta ce abin da bai taba
tsammani zai zama amsar tambayarsa ba. Ya
riga ya san idan da abu guda da ta tsana a
rayuwarta bai wuce amaryarta Zainab ba. To,
amma jin sabanin abin da ya yi tsammani sai ya
yi sauri ya ce, "Ni dai na san wannan shiga ba
banza ba, akwai wajen zuwa ko?"
Ta langwabar da kai akan majinginar kujerar kana
ta kuma fari da fararen idanunta, wadanda sau
da
yawa ta san fari da su kan yi tasiri wajen jan
hankalinsa. Sannan da sababbiyar murayarta ta
yaudara ta ce, "Alhaji, ina so na je unguwa ne
idan an jima."
"Har ina kenan?" Ya bukata bayan ya dauke
kansa daga kallon ta zuwa sakalallen hotonsa da
ke kafe jikin bango, jin abin da bai taba
tsammanin shi ya kawo ta ba.
Abin da ya riga ya sani ne, ta sha fita zuwa
unguwa ba tare da saninsa ba. To, amma yanzu
me ya sa ta zo tambayar sa. Sai dai bai bari ta
gane abin da ke cikin ransa ba, ya ci gaba da
tambayar ta. "In ce dai babu nisa ko?"
"Babu nisa sosai...wata gaisuwa na ke son
zuwa."
"Gaisuwa?" A wannan karon ya dawo da dubansa
gare ta.
Ta gyada kai, "Wallahi kuwa."
"Allah sarki." Ya ce ya na sosa kai, "Wane ne ya
rasu?"
"Wallahi dan gidan wata aminiyata ce ya rasu
daren jiya, da sassafen nan aka sanar da ni." Ita
da kanta sai da ta ji wani iri abu banbarakwai a
bakinta saboda mamakin karyar da ta shirga cikin
kankanin lokaci.
Ya nisa cikin tausayawa ya ce, "Allah ya ji kan
rai, ya gafarta masa...mu kuma ya kayuta namu
zuwan."
"Amin-amin" Ta amsa kai tsaye kamar gaske.
"Wannan ai babu damuwa Hajiya." Ya ci gaba,
"Idan kin gama shiryawa kawai direba ya kai
ki..."
"A'a Alhaji". Ta katse shi, "Babu bukatar mu tafi
da direba a wannan tafiyar don kuwa ni da
kawata da mu ka jima ba mu hadu ba za mu je,
kuma tuntuni ma na riga na yi mata bayanin ni
zan ja motar." Ta dan yi shiru ta natunanin yadda
za ta dire karyar da ta shiryo. Ta ci gaba a
wannan karon da rawar baki, "Har gardama fa
mu
ka yi, ta naban iya ba, ina cewa na iya! Ka na so
ta yi mini...dariya ne ko kuwa ya ya?"
"A'a Hajiya ba na kaunar haka. Abin da ki ka riga
ki ka sani ne Tunda Allah ya zurta ni na ji ba na
kaunar iyalina su ja mota, don ni na dauki hakan
abin kunya a gare ni. Kuma koya mu ku mota ma
da na sa aka yi, ai ba don ku dinga ja ba ne,
saboda kawai bacin rana." ya tsagaita ya na
daidaita numfashinsa, a halin yanzu kuma ya
hade fuskarsa sabanin baya.
Hajiya Rukayya ta dukar da kai jin dogon jawabin
da ya yi na kin amincewa, wanda da ma ta yi
zaton samun sa.
"Da alama idan ki ka saki za ki yi wa kanki
sakiyar da babu ruwa, Muddin ki ka bari Alhaji ya
ce lallai direba ne zai kai ki babu yadda za a yi
asirinki ya rufu. Ki san duk yadda za ki yi a
matsayinki na ya mace ki shawo kansa. "wani
sashe a zuciyarta ya rada mata.
Ta cira kanta a hankali ta dube shi. Da raunin
murya ta ce, "Haba Alhaji." A hankali sai ta matsa
kusa da shi sosai, wanda
har ya na iya jin hucin numfashinta a gefen
fuskarsa, "Mene ne abin jin kunya don mun ja
mota da kanmu? Ai ni kuwa ina ganin babu
kasawa ga hakan.
Kuma ma idan ka na tunanin kasawa ne, wa zai
kula har ya gane cewa ni ce ke jan mota?"
Ya girgiza kai, "Gaskiya Hajiya ni ba na son
abin..."
"Kai don Allah Alhaji". Ta katse shi bayan ta kara
matsawa kamar za ta shige jikinsa. Ta kara
sauke muryarta kasa sosai kamar mai rada,
"Alhaji don Allah ka amince...yau daya dai." Ta
dan hade fuska, da shagwaba ta ci gaba,
"Gaskiya idan ba ka amince ba raina zai iya baci,
kuma za mu bata."
Duk da ta yi wata yar malalaciyar dariya a
karshen maganar tata wadda ke nuna da wasa ta
ke abin da ta fada, hakan bai hana shi shiga
fargaba ba. Haka kawai sai ya ji gabansa na
faduwa, a sannu kuma sai ya ji zuciyarsa ta
soma amincewa da bukatar ta.
Fahimtar ta da hakan ne ya sa ta furta a hankali,
"Alhaji ka amince?"
gyada kai kawai ya yi ba tare da ya furta komai
ba.
"To, ai kai kawai ka gyada mini ba ka ce komai
ba." Ta jefa shagwaba cikin muryarta, "Ka yarda
na je?"
Ya kuma gyada kai, kana a hankali ya ce, "Na
yarda ki je."
Ta mayar da kanta ta jingina jikin majiginar
kujerar saboda dadin da ya mamaye zuciyarta. A
hankali ta shiga furta, "Na gode, Alhaji, Allah ya
kara dankon soyayya tsakaninmu." Wannan kalma
ta kara tsunduma Alhaji Basiru cikin tsananin
mamaki.
***
Tun sa'ar da su ka kama hanyar zuwa gidan
malamin tsibbun Hajiya Rukayya ke jin dadi ta
nata washe hakora kamar wadda akawa wani
babban Albishir, saboda tunaninta na ganin cewa
yau ne za ta kawo karshen abin da ya tsokane
mata idanu. Kuma ya ke damunta wato kishiyarta
da danta mujahid.
Koda yake a yanzu hankalinta ya fi karkata ga
mujahid din, ta fi so ta ga babu shi kafin
mahaifiyarsa musamman mada Baraka ta haska
ma ta illarsa, na cewa ya na da gadon mace biyu.
Ta dubi Baraka da ke zaune gefenta na dama
gaban motar, daidai lokacin da ta fada wani
kwazazzabo,
"Baraka ni fa na fara ji a jiki na bukata ta biya,
Ba ki ji yadda zuciyata ke tumbatse da farin ciki
ba."
"Ahaf! Wannan ma kadan kika ji, sai ma bukata
ta biya tukunna." Baraka ta ce ta natabe baki,
"Don ma kin ce dan kawai ki ke so a kawar, da
da uwar ai da farin ciki naki ya fi haka."
"ke dai yi shiru tawa". Hajiya Rukayya ta ce gami
da dora yatsanta a baki "Ina so mu yi a hankali
ne idan yanzu mu ka ce za mu yi mai gaba daya,
ba makawa sai na shiga zargi da tuhuma kuma
zai yi wuya na kubuta, amma idan mu ka dauke
su daya bayan daya, sai ki ji shiru kamar an
shuka dusa, babu wani dan iska da zai kalle ni,
balle har ya zarge ni."
"E to, ke ma kin yi tunani. "Baraka ta ce sannan
ta daga yatsanta manuni, ta yi wa Hajiya
Rukayya nuni da wata yar karkatacciyar bishiya
da ke gabansu kadan,
"Idan kin isa ga bishiyar can sai ki tsaya, mun iso
gidan."
Hajiya Rukayya ta gyada kai ba tare da ta ce
komai ba, sannan ta ce, "Da ma yanzu na ke
shirin tambayar ki ganin cewa muna nisa cikin
wannan uban daji."
Ta daka mata harara, "Ke kuwa akwai ki da tsoro
Rukayya. Ina wani daji a nan? Ai yanzu babu
dajin, ba ki ga har gidaje sun fara yawaita a cikin
sa ba. Tab! Da a ce yan shekarun baya ne ki ka
zo, da ba za ki kira wajen da daji ba yanzu."
"Allah kawar?"
Hajiya Rukayya ta ce da mamaki lokaci guda
kuma ta na kara nazarin dajin.
Dajin ya na da fadi da tsawo, sannan akwai yar
duhuwa duk da cewa dai akwai yan gidaje tsilla-
tsilla.
"Ina, ai yanzu ina dajin ya ke." Baraka ta ce cikin
murmushi bayan sun mayar da murafen motar
sun rufe.
Ta dubi Hajiya Rukayya ta yi kasa-kasa da
murya, cikin rada-rada ta ce, "Sai ki yi shiri,
kuma
ki iya bakinki, ki san abin da za ki ce don nan
mun zo wurin da ba a shiririta."
"To, an gama...kar ki ji komai." Hajiya Rukayya
ta amsa a tsorace, ita ma cikin rada bayan ta
dafe kirjinta, alamun tsoro karara a fuskarta. A
lokaci guda kuma ga rashin mamakinta sai ta ji
zuciyarta ta soma harbawa, domin ita tun da ta
ke ba ta taba ganin daji irin wannan ba a fili, sai
dai ko a akwatin talabijin.
Cikin fargabar da matsananciyar bugun zuciya ta
dafawa Baraka baya su ka nufi dan
durkushasshen gidan.
Kadan ya rage fitsari ya kufce ma ta sa'ar da ta
taka wasu busassun ganyaryaki su ka bada wani
amo.
Turus su ka ja su ka tsaya cak kamar dawakan
da aka ja wa linzami. Da sauri su ka fara waige-
waige kamar barayi sakamakon tsawar da su ka
ji an yi mu su kamar daga sama yayin da su ka
shiga gidan.
"Ku tsaya nan, kar ku kuskura ku kuma takawa,
idan ba haka ba fuskokinku za su koma keya,
mutanen banza!" muryar da har yanzu su ka
kasa
ganin mai ita ta ci gaba da gargadin su.
Tsananin tsoro da fargaba ya sa su ka soma
tsuma kamar wadanda ake kada wa gangi. Nan
da nan dakakkiyar zuciyar da Baraka ke tunkaho
da ita ta bi ruwa.
Karar sukuwar dokin da su ka ji daga bayansu ya
sa su juyawa lokaci guda, kana da gagawa su ka
tsuguna sakamakon ziyarar da wani kakkarfan
haske ya yi w idanunsu. Sannu a hankali sai su
ka fara ganin wata irin
halitta a gabansu, wadda ba za su iya tantance
wa zuciyarsu fasalinta ba. Abu guda da su ka fi
lura da shi sosai ga halittar shi ne, ta fi kama da
dodon da su ka sha ji a tatsuniya fiye da komai.
Halittar ta fashe da wata irin shaidaniyar dariya,
a hankali-a hankali kuma sai ta soma sauya
kama, babu jimawa sai ta dawo siffar mutum
sosai. Mutumin da ya maye gurbin halittar baki
ne kato, sanye a jikinsa wasu bakaken kaya ne
masu ratsin ja. Ya kuma fashewa da dariya
tsawon lokaci, sannan ya soma da duban su ya
na hura hancinsa mai kama da begila. Kusan
minti guda ya yi ya na duban su, daga bisani ya
ce da wata budaddiyar murya, "Kai mutanen
banza. Shagalallu, bukatar da ku ka zo mini da
ita mai sauki ce, ba kuma na bukatar ku sanar da
ni komai game da al'amarin domin tuni dan
marayan aljanu ya kawo min labarinku." Ya yi
shiru ya na wani gurnani mai ban tsoro. Su ka yi
ajiyar zuciya lokaci guda kamar wadanda aka
watsa wa sassanyan ruwa, cikin mamaki su ka
fara satar kallon junan su.
"Lallai matsalar ki." Ya nuna Hajiya Rukayya, "Bai
wuce ta kishiyarki da danta ba, me ki ke so a yi
mu su?" Da tsawa ya bukata.
Tsawon lokaci su ka dauka ba su amsa ba
saboda tsananin tsoro. Sai daga bisani Baraka ta
zura hannu a sace ta zunguri Hajiya Rukayya,
cikin rada ta ce, "Ki fada masa abin da ya kawo
mu."
Ba ta yi gardama ba. Take ta sanar da shi
bukatarta ta son a fara kawar ma ta da mujahid.
Bokan ya tuntsure da dariya, kana ya yi wata irin
kakkarfar ajiyar zuciya, "Tabbas kin zo da
al'amari mafi sauki a gare ni, kuma karamin abu
wanda ba ni ya kamata na yi shi ba saboda
saukin sa, duk da cewa dai ke mai wahala ne a
gare ki matukar ki ka kuskure wa abin da zan
umarce ki." ya saurara ya na zare idanu.
Hajiya Rukayya ta dafe kirji jin abin da ya ce.
"Hajiya". Ya dawo da hankalinta gare shi cikin
murya mai tsoratarwa. "Dole ki yi taka-tsan-tsan
da abin da zan gaya miki tun kafin na sanar da
ke, domin ko ya ya ki ka kurkure na hango miki
nadama a rayuwarki." Ya yi shiru kana ya ci gaba
da dariya.
Su kuwa babu abin da su ke yi sai kyarma.
"Hajiya" ya kuma kiran sunanta, wannan karon
muryar ta fi ta baya tsoratar wa, "Matso nan na
sanar da ke." Ya miko ma ta hannunsa.
Ta juya da sauri ta dubi Baraka a tsorace. Kafin
ta ce wani abu Baraka ta ce, "Ki matsa mana, kar
ki fa bata ma sa lokaci." Ita ma a tsorace ta yi
maganar.
Take ta ji wani abu mai kama da kwallon kafa ya
taso daga cikinta zuwa wuyanta. Ba don ta yarda
Baraka na kaunar ta ba, da sai ta ce ba ta da
babbar makiyiya irin ta, don a iya tunaninta babu
wanda zai ce ta matsa kusa da wannan Boka sai
makiyinta.
Babu yadda ta iya, haka ta matsa kusa da Bokan
a hankali kamar wadda ke rabar wuta.
Wani wari ne ya fara dukan hancinta daidai
lokacin da ya miko dogon bakinsa fa kunnenta.
Duk da cewa abin da ya ke fada wani abu ne da
ta jima ta na neman sa, hakan bai hana ta jin
kamar za ta amayar da kayan cikinta ba, saboda
tsananin warin bakinsa "Rike wannan!" Ya ce da
kaushin muryarsa bayan ya gama yi mata radar.
***
Da alama tafkeken ruwan saman da aka kusan
kwana ana tafkawa a daren na jiya, kamar da
bakin kwarya, shi ya haifar da wadatacciyar iska,
iskar da ke kadawa fil-fil-fil babu alamar
tsagaitawa. Iskar za ta fi gamsar da mutum idan
har aka yi sa'a ya yi wanka, kamar yadda wasu
su ke hasashe. To amma kuma ga mamakin
wasu tsiraru daga cikin mutanen da ke mantawa
da kudurar Ubangiji Madaukaki, korafi da
mamakin ruwan su ka rika yi su na cewa, wai
kasa ta tsotse makekan ruwan da aka maka.
Hakan ya haifar da rabuwa a tsakanin su, yayin
da wasun su ke cewa, meyiwa kasar ta tsotse
ruwan ne saboda jimawa da aka yi ba a samu
ruwan ba.
To, ko ma dai mene ne, Allah shi ne ya saukar
da
ruwan, kuma shi ya kaddara kasar ta tsotse shi
kasancewar sa Mai yin yadda ya so.
A daidai wannan lokaci da iskar ke ci gaba da
filfilwa, direba Lukman, direban gidan Alhaji
Basiru na daya daga cikin mutanen da ke jin
dadin ta, duk kuwa da cewa kwance ya ke a daki
abinsa ya na ta sake-saken abin da ka je ya zo.
Sannu a hankali ya yi mika akan figaggiyar
katifarsa mai kama da takkaken silifas, sannan ya
yi salati ta cikin iskar hammar da ke fita daga
bakinsa.
Daga kwance ya langwabar da kansa gefe guda,
ya kai dubansa ga fuskar agogon da ke makalr a
jikin bango. Ya yi tsaki ganin har zuwa lokacin
takwas ba ta yi ba.
Ya kuma dauke kansa a hankali daga duban
agogon zuwa ga rufin dakin kamar mai kidayar
hudojin da ke jikin kwanon, lokaci guda kuma
tunani da mamakin kiran da Hajiya Rukayya ta yi
masa a yammacin jiya su ka lullube masa zuciya.
"Lukman na kira ka ne saboda na shaida maka
cewa gobe ba na so ka zo kai yara makaranta..ni
zan kai su. Sai dai ina so ya zama kai za ka
dawo da su. Amma fa ka sani hakan ba ya na
nufin kullum ba ne, daga gobe shi kenan"
Maganar da Hajiya Rukayya ta fada masa a jiyan
ta ci gaba da kewaya zuciyarsa.
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
Bakin Kishi 2
Posted by ANaM Dorayi on 08:18 AM, 29-May-15
"To, mene ne dalilin Hajiya na yin haka?"
Tambayar da ya ke yi wa kansa kenan a duk
sa'ar da ya tuno da maganar, to amma har zuwa
yanzu ya rasa samun amsa.
A hankali ya dogara hannunsa biyu ya tashi
zaune a karo na farko tun lokacin da ya kwanta
bayan ya dawo daga sallar Asuba.
Abu guda da ya fi amincewa da shi a zuciyarsa
shi ne, ba banza Hajiya Rukayya ta shirya hakan
ba. To idan kuwa hakan ne babu shakka ya
kwadaita da ya san dalili.
"To, a ina zan san dalilin?" Wannan karon da
sauri ya furta kuma a fili.
Nan da nan sai ya fara zargin kansa da yin Allah
wadai, da ya kasa tambayar ta dalili a jiyan.
"Gaskiya na yi sakaci, tun a jiya ya kamata na
tambaye ta dalilin ta na..." Tunaninsa ya katse
da ya tuno da abin arzikin da ta yi masa a jiyan.
Ya laluba aljihun gaban rigarsa da sauri kamar
mai yin rige-rige da wani. Har yanzu kudin na
nan.
"Ga wannan ka karya kumallo da safe a
maimakon wanda ka ke yi anan." ya tuna abin da
ta ce da shi lokacin da ta miko masa kudin.
"Har dubu daya Hajiya?" Ya tuna abin da ya ce
da
ita lokacin da ya karba ya kirga.
Abin da ya riga ya sani ne tun farkon daukarsa
aiki a gidan, kyautar Hajiya Rukayya ba ta wuce
Naira Hamsin, a ta yi yawa dari.
"Kai gaskiya da walakin." ya kara furtawa a fili ya
na duban kudin. Bayan tsawon lokaci ya na
duban su ya mayar aljihu, sannan ya kuma
komawa ya kwanta ya na fadin, "Bari na jira
lokacin da ta ba ni ya cika na ga abin da ya
samu a gidan." Ya ja tsohon mayafinsa mai kama
da matacin koko ya rufa. A can cikin zuciyarsa ya
na Allah-Allah karfe daya ta yi.
Da kyar da curewa guri guda kamar kunkuru
mayafin ya ishe shi.
***
Karfe takwas daidai agogon da ke makale jikin
bango cikin makeken falon ya saki wani
daddadan kara, karan da ya ja hankalin Zainab
da
yaran guda uku da ke cikin falon zuwa fare shi.
Yaran ba wasu ba ne, Mujahid ne danta da
Hauwa'u da Sailuba, 'yayan Hajiya Rukayya.
Yanzu kasan sa'a guda kenan su ka share su na
zaman jiran zuwan direba Lukman, don ya kai su
makaranta, amma shiru ka ke ji kamar an aika
bawa garinsu. Wannan al'amarin ya fi cusa
zainab cikin damuwa.
Al'adarta idan ta yi wa Mujahid wanka, ba ta iya
yin komai sai ta ga Lukman ya zo ya tafi da su
makaranta, wasu ranakun ma kafin ta gama
shirya shi ya ke zuwa, amma sabanin kullum yau
ga shi ta gama kammala masa komai, sama da
sa'a guda bai zo ba.
"To, mene ne ya hana shi zuwa?" Abin da ta ke
yawan tambayar kanta kenan, amma ta kasa
gane dalilin. Abu guda dai da ta fi yarda da shi
shi ne, koma dai mene ne ya hana direban zuwa
to ya na da karfi.
Cikin wannan hali na damuwa da Zainab ke ciki
Hajiya Rukayya ta shigo falon da sauri kamar
wadda aka biyo a guje.
"Me ya faru har yanzu ba ku tafi makaranta ba?"
Wannan ita ce maganar da ta fara fita daga
bakinta a maimakon sallama.
"Wallahi har yanzu direban ne bai zo ba, ga shi
kuma har sun yi latti." Zainab ta amsa ma ta
cikin girmamawa, duk da cewa ba ita ta tambaya
ba.
"To, ina ruwanki? Ke na tambaya ko kuwa ya ya,
Zakakura?"
Zainab ta kada kai, "Allah ya huci zuciyarki, da
ma gani na yi kin yi tambaya kuma duk cikin su
babu wanda ya amsa, shi ya sa."
Hajiya Rukayya ta kuma doka ma ta harara,
"Sannu mai baki, su kuma 'yayan nawa ina ki ka
kai min bakin nasu? Ko ki na so ki danganta min
da wannan dolon yaron naki, wawa marar baki?"
Ta juya ta naduban Mujahid a wulakance.
Zainab ta cira kai ta dube ta, makale a fatar
bakinta wani dan murmushi ne da Hausawa ke
yiwa lakabi da yake, "To, don Allah ki yi hakuri,
na ji na yi miki laifi, amma surutun ya isa
haka..."
"Bai isa ba!" Ta katse ta, "Na ce bai isa ba!" Ta
tattara hankalinta gare ta, kana ta dora hannu a
kirju, "Ni ki ke cewa surutun ya isa haka? Ni ce
ma mai surutu?"
Shiru ba amsa daga Zainab.
Hajiya ta kwashe wata irin dariya da ta tuno da
shirinta da ke a kasa, "Babu komai, kin susa
dainawa." Ta ce a ranta. A fili kuma sai ta ce,
"Na ga alama wuyanki ya yi kauri yarinyar nan."
Ta tsagaita da dariya ta shiga gyada kai, "Amma
ba komai, ci gaba za ki kwashi kashinki a hannu
nan ba da jimawa ba." Ta juya ga yaran, "Ku
tashi mu tafi ni na kai ku. Shi kuma Lukman idan
ya zo ya fada mini dalilin kin zuwan nasa."
Hauwa'u da Sailuba su ka mike kamar ba sa so,
fuskokinsu cike da damuwa. Duk da cewa
kananan yara ne da ba su haura shekaru tara-
tara ba kasancewarsu an haife su yan biyu, su na
matukar nuna damuwa da abin da mahaifiyarsu
ke yi wa Zainba din, wasu lokutan ma har hakuri
su ke bawa Zainab din idan mahaifiyarsu rufe ta
da fada.
Su ka rufa ma ta baya. Daf da za su fice daga
falon ne ta juyo ta dubi Mujahid da har yanzu ke
zaune kusa da mahaifiyarsa, "Kai kuma
algungumi ba za taso mu tafi ba, ka makale a
jikin uwarka ka na duban mutane dai-dai?"
lokacin da suka shiga makarantar tuni dalibai sun
jima da shiga azuzuwa, wasu ma har sun fara
kara tu, amma duk da haka bai hana Hajiya
Rukayya tsayawa wani dan madaidaicin shagon
sayar da kayan tsotse-tsotse da lashe-lashen
dake cikin makarantar ba. "Hajiya Na manta ban
tambaye ki guda nawa ba".
A wannan karon kafin ya dafa motar ya fada.
Ta yi murmushi, "Ba mu biskit din guda uku,
alewar kuma guda biyu."
Ya so ya ce ma ta ta yi kuskuren fadar alewa
biyu a maimakon uku ganin yaran su uku ne,
amma sai ya kyale, sai da ya je ya kawo, sannan
ya yi ma ta abin da ya kira wo da tuni, "Hajiya
kin manta kin ce alewa biyu na ga yaran su
uku..."
"Ka ga saurara." Ta katse shi, "Ban ce ma na
manta ba, kai dai nawa ne kudinka?"
Bai ji haushi sosai ba don ya san shi ne ya yi
shisshigi. "Naira dari da hamshin." ya amsa
daidai lokacin da ya mika ma ta.
"Ungo." ta miko masa sabuwar Naira dari biyu ko
kari babu bayan ta karba. Sannan ta juya ga
yaran da ke zaune bayan motar ta fara raba mu
su.
Duk da cewa saurayin ya sa hannu a aljihu ya na
kokarin dauko ma ta canji, hakan bai hana shi
jifan tsuntsu biyu da dutse guda ba, don kuwa da
wutsiyar idonsa ya na kallon yadda ta ke rabon,
ya san dai dole daya zai rasa, kuma za a bukaci
ya kawo.
A kan Mujahid alewar ta kare bayan ta gama
raba
mu su biskit din.
Mujahid ya dube ta, ya dubi yan uwansa ganin
alewar da ta kare shi bai samu ba, alamun
damuwa gauraye da na kuka su ka bayyana a
fuskarsa.
"Yi hakuri Mujahid, kai bari na ba ka taka alewar
mai dadi, ka ji." Ta ce ta nayin wani irin
murmushi, sannan ta bude. 'yar karamar jakarta
da ke ajiye gaban mota, ta dauko alewar, "Rike,
da kyau, kar ka kuskura ka ba kowa. Kowa ya
sha tasa. Kun ji ko?" Ta gargade su.
Su ka gyada kawunansu cikin gamsuwa kuma
hakan ne ya sa saurayin ya dauke kansa cikin
fitar da rai cewa zai sake samun ciniki.
"Ga canjinki Hajiya." Ya ce bayan ya gama
kirgawa. "jeka ka rike" Ta ce da shi cikin kosawa,
kana ta ja motar ta yi gaba.
Saurayin ya bi motar da kallo sannan ya kece da
dariya a fili ya ce "Kai kudi ma dai ba su da
kama...dubi wannan mummunar mata haka
kamar an sassako cikin wannan zundumemiyar
mota.
***
Sau daya kawai ya latsa hon din motar babbar
kofar gidan ta bude. Cikin hanzari direba Lukman
ya shige da motar cikin yalwatacciyar farfajiyar.
Ba yanzu ya soma hanzarin ba, tun lokacin da ya
bar gida ya nufi makaranta da zummar dauko
yaran ya ke ta hanzari shi ya sa yanzu da ya
danna hon din sau daya ya ga kofar ta bude ya ji
dadi a ransa, har ma zuci ya shiga yabawa
kulawar Malam Bukar akan aikinsa, duk kuwa da
cewa wani lokacin sai ya yi hon sau fiye da goma
bai bude ba ya na cen ya na ta gyangyadinsa.
Kamar yadda ya saba, cikin sauri ya karbi
jakunkunan da ke hannun su Hauwa'u bayan ya
mayar da murafen motar ya rufe. Kai tsaye ya
wuce cikin gidan, yaran su ka rufa masa baya.
Duk wannan sauri da ya ke yi, ya na yin sa ne
don kyautata zatonsa na samun bakon abu,
musamman saboda hana shi zuwa gidan da
Hajiyya Rukayya ta yi a safiyar yau.
Hanzarinsa ne ya ragu lokacin da su ka yi daf da
falon ya ji ana hira da shewa a ciki. Sallama ya
fara kafin ya daga labulen.
"Wa'alaikas salam." Muryar matan biyu ta amsa
sallamar daga cikin falon. Zainab ce da wata
kawarta da ta kawo ma ta ziyara, mai suna
Barista Hannatu Muhmud.
Barista Hannatu kawar Zainab ce tun su na
makaratar sakandire. Sun shaku da juna matuka,
har ya zamto duk inda su ka nufa za ka ji ana ce
mu su yan biyu. Amma a lokacin da su ka gama
sakandire sai su ka samu rabuwar ra'ayi. Ita
Zainab ta sauya darasin karantunta ta wuce kai
tsaye ga fannin koyon bada kariya ga al'uma,
wato lauya. To amma wani abin mamaki dan
sha'awa ga kawayen biyu, wannan rabuwar
ra'ayi
ba ta shafi kawance da son junansu ba. Duk da
haka sai su ka ci gaba da ziyartar juna akai-akai,
har kawo yanzu da kowannen su ya gama
karatunsa kuma ya ke cin moriyar karatun.
Haduwar wadannan kawaye ta na zama abin
sha'awa, don da kyar su ke iya rabuwa saboda
son juna. Yau ma tun karfe goma na safe
Hannatun ta zo, kuma kamar yadda ta saba sai
karfe biyar ko fiye da haka ta ke barin gidan.
Shi ya sa yanzu da direba Lukman ya zo ya yi
mu su sallama su ka ji kamar ya shiga
rayuwarsu, don duk sa'ar da su ka hadu ba sa
kaunar wani abu ya katse mu su hirarsu.
Suka daubi kofar shigowa falon bayan sun amsa
sallamar.
Lukman ya daga labule ya shigo.
Mamaki ne ya fi rinjayar komai a fuskar Zainab
bayan ta gane Lukman ne ya dauko yaran daga
makaranta.
Shi ma alamun mamaki sun bayyana a fuskarsa
sai dai shi nasa bai yi tasiri ba saboda sanin
cewa dole ne ko wane ne zai yi mamaki
musamman ma idan ka yi la'akari da cewa ba shi
ne ya kai yaran makaranta da safe ba, kai hasali
ma bai zo gidan ba tun safe. Bai samu damar
magana ba har Zainab ta ce, "Lukman daga ina?"
Tambayar ba ta ba shi mamaki ba.
"Daga makaranta na ke na je na dauko su ne." ya
amsa kai tsaye bayan ya tsuguna.
Mamakin ta ne ya karu. Ta dubi Hannatu da
zummar ta yi magana, amma kafin ta yi sai ta
riga ta da cewa,
"Lafiya na ga ki na mamaki don ya je ya dauko
su daga makaranta, ba aikinsa ba ne?"
"Aikinsa ne, amma..."
"Amma me?" Hannatu ta katse ta. "Amma gani
na yi cewa ba shi ya kai su ba,
kuma ma bai zo gidan ba yau kwata-kwata!"
Zainab ta amsa lokaci guda kuma ta mayar da
duban ta ga Lukman din. Hannatu ba ta fahimci
abin da ta ke nufi ba, don haka ba ta sake yin
magana ba, maimakon hakan ma sai ta ci gaba
da sauraron su.
"Lukman me ya sa yau ba ka zo ba?" Tambayar
ta so ta rikita shi, amma koda ya tuno da gargadi
da kuma kudin da Hajiya Rukayya ta ba shi sai
ya ji ya dan nutsu.
"Ba ni da Lafiya Hajiya...mu..mura ce ke damu
na
Hajiya..dauriya ce kawai irin tawa ta sa na
fi...fito." ya amsa a marairaice murya na rawai.
Nan da nan alamun mamakin su ka yi kaura da
ga fuskar Zainab yayin da na tausayi su ka maye
gurbin, jin abin da Lukman ya ce.
Ta girgiza kai cikin tausayi sannan murya a
tausashe ta ce, "Allah ya saukake Lukman, sannu
ka ji?"
"Amin." Ya amsa lokaci guda kuma ya shafi kudin
da ke aljihunsa wanda Hajiya Rukayya ta ba shi,
a cikin zuciyarsa ya ce, "Yanzu har na yi aikin
Naira dubu? Kai lallai wannan auki da sauki ya
ke, da a ce zan rika samun irin sa tsawon wata
shida ai da na bar aiki na koma ni ma na kwanta
na dinga yi wa kudin cin kadan har su kare, na
san dai kafin lokacin zan yi kaurin wuya da
kumatu da kuma tumbi kamar na mai gidana."
***
Sabanin kowace tana da Alhaji Basiru ya saba
dawowa gida karfe shida na yamma, yau sai ga
shi ya dawo tun karfe hudu, meyiwa hakan na da
alaka da shirye-shiryen tafiyar da zai yi zuwa
kasar Ingila. Kuma kamar yadda ya saba dawowa
shi kadai, yau su uku ne, shi da kaninsa wanda
su ke uwa daya uba daya da ke da zama a garin
Katsina mai suna Alhaji Sambo da kuma wani
abokin harkarsa kuma amininsa Alhaji Gali.
Aminan biyu su ka samu a falon (Zainab da
Hannatu) har zuwa yanzu su na zaune su na
hira.
"Sannun ku da zuwa." Zainab da Hannatu su ka
fada lokaci guda cikin sakin fuska da walwala,
bayan sun amsa sallamar magidantan uku.
Doguwar gaisuwa su ka yi kafin daga bisani falon
ya yi shiru. Alhaji Sambo shi ya kau da shirun da
tambayar Zainab. "Hajiya Zainab amarya, ina
uwargidan ne?"
Ga ta nan tafe." Muryar Hajiya Rukayya ta ratso
falon kamar daga sama, wanda hakan ne ya ja
hankalinsu zuwa kofar shigowa falon daidai
lokacin da ta dago labulen falon ta shigo.
"Yar halak! Yanzun ann na ke tambayar ki." Alhaji
Sambo ya ci gaba ya na duban ta cikin fara'a.
"Ni ma ai ina jin ka, shi ya sa na amsa ma." Ta
ce ta na yin wani dan asirtaccen murmushi,
kamar ba ta so.
"Ai daman na dauka kin fita ne ba tare da kin
tambaye ni ba na dau mataki idan kin dawo." Ya
kuma cewa cikin dariyar tasa, sai dai wannan
karon ba shi kadai ba, kusan dukkannin su babu
wanda bai dara ba, idan ka dauke ita Hajiya
Rukayya da ta turbune fuska. Wannan wani wasa
ne da Alhaji Sambo ya saba yi wa Hajiya
Rukayya, wasan da ake wa lakabi da na kanin
miji.
Hajiya Rukayya ta samu daya daga cikin jerin
kujerun da ke gewaye da falon ta zauna, sannan
su ka gaisa cikin fara'a da sakin fuska. Ko
shakka babu sakin fuskarta na da alaka da ganin
bakin biyu, don kuwa idan da akwai abin da ya fi
wuta zafi, zuciyar Hajiya Rukayya ta fi shi zafi a
wannan rana ganin cewa duk abin da ta shirya
akan Mujahid ya dawo daga makaranta lafiya.
Ranta ya kuma kuna sa'ar da ta ji muryar
Maigidanta ta ratsa dodon kunnenta da cewa,
"Hajiya na zama mu ka zo yi ba abinci kawai mu
ka zo ci kafin mu wuce, kin san karfe biyar
jirginmu zai tashi." Duk da cewa muryarsa a
kwancw ya yi maganar hakan bai hana jin kamar
ta ce masa ba za ta kawo ba domin gani ta ke,
raini ne a ce ta tashi ta kawo abinci bayan ga
Zainab da ke matsayin kanwarta.
Haka dai ta daure ta danne fushinta, ta tashi ta
nufi kicin ta nakunkuni, shi ma kuma wannan
duk
ganin idanun bakin ne.
Kamar wadanda ke jiran fitar ta, yaran uku su ka
shigo falon a guje, Mujahid a gaba, Hauwa'u da
Sailuba biye da shi.
Turus! Hauwa'u da Sailuba su ka ja su ka tsaya
kamar wadanda aka kira sunansu daga baya,
wannan kuwa ya biyo bayan ganin mahaifinsu da
su ka yi babu zato babu tsammani. Shi kuwa
Mujahid bai tsaya ba har sai da ya dangana da
mahaifin nasu, ya fada kan cinyarsa ya na dariya.
"Kai, ua ya lafiya? Mene ne kuke bin sa a guje
haka?" Alhaji Sambo ya fada.
"Ba shi ne ya ce wai ya girme mu ba." Hauwa'u
ta amsa da wata shagwababbiyar murya.
Gaba daya su ka bushe da dariya.
"To, mene ne don ya ce ya girme ku? Banda abin
ku wa ya ke son girma?" A wannan karon Barista
Hannatu ce ta yi maganar cikin ragowar dariyae
da su ke yi.
"To, ai karya ya ke yi...mun fa girme shi Wallahi."
Sailuba ce ta fada ita ma cikin shagwaba ta na
hararar Mujahid din.
"To, ai shi kenan. Ku yi hakuri kun girme shi."
Alhaji Basiru ya ce ya na shafa kan Mujahid da
har yanzu ke kwance kan cinyarsa. Ya ci gaba,
"Zan yi tafiya amma idan zan dawo karami kawai
zan sayo wa kayan dadi, kun yar..."
"E, na yarda ni ne karami, ni za a sayo wa"
Mujahid ya katse shi ya na tafa hannu.
"A'a, mu ba mu yarda ba" Su ma su ka fada. Da
wannan kace-nacen su ka cika falon. "To, ku
dakata, ya isa haka." ya dakatar da su
"Kowa za a sayo masa...da me da me ku ke so?"
"Ni ne zan fara Baba." Mujahid ya yi sauri ya
fada bayan ya yi zumbur ya mike daga kwanciyar
da ya yi.
"To fadi." Ya ba shi izini da gaggawa don gudun
kar su Hauwa'u su ce ba su yarda ba. Yanzu
kusan falon ya yi shiru kowa yana sauraron abin
da mujahid din zai ce ya na so.
"Ina son a sayo min jirgi da mota, uhm...uhm da
Bindiga da kuma kambos..." Gaba daya su ka
kuma tintsire wa da dariya.
"Babbar magana." Alhaji Basiru yace "mujahid
sakon naka babba ne." ya juya ga su Hauwa'u,
"Ku kuma fa me za a sayo mu ku?"
Sailuba ce ta fara cewa, "Ni Dan kunne da Sarka
da kwabashu (Cover Shoe) na ke so."
Ba ta samu sabani da Hauwa'u ba, domin ita ma
abin da ta lissafo kenan, sai dai karin abu guda
akan na Sailubar, shi ne Alewa mai zaki, wanda
kuma lokaci guda shi ne abin da ya tuna wa
Mujahid alewarsa ra safe da Hajiya Rukayya ta
saya mu su a makaranta. Nan da nan ya tuna,
bai samu damar shanye tasa ba wancan lokacin
saboda shiga aji da ya yi ya tarar ana karatu
malaminsu ya hana shi sha, ya ce ya sa a aljihu.
Allah da ikonsa kuma ya manta da ita sai yanzu
da sakon Hauwa'u ya tuna masa.
"Lah! Baba ni ma ina da Alewata wadda Momi
babba ta ba ni da safe a makaranta."
Bai saurare shi ba don a lokacin hankalinsa ya
tafi ga Barista Hannatu da ta ce za ta tafi gida.
"Tun yanzu za ki tafi Hannatu?" Alhaji Basiru ya
ce ya na duban ta, "Ba za ki bari sai an jima ba?"
Ta yi dariya lokacin da ta ke yunkurin mike wa,
"Babu komai Alhaji, ai na dan jima anan, sai dai
kuma an kwana bi..." Mujahid ne ya katse ta da
kukan da ya soma ganin ba a saurari abin da ya
ke fada ba.
"Kai! Wai mene ne haka?" Alhaji Basiru ya
tambaye shi da tsawa.
"Alewata za a dauko min." ya amsa cikin kuka.
"Ta na ina?" Bukata daga Alhaji Basiru.
"Ta na cikin aljihun wandon makarantana." ya
amsa ya na murtsuke idanu bayan ya tsagaita da
kukan.
"Zainab don Allah je ki dauko masa kar yua dame
mu."
Umarni daga Alhaji Basiru.
Zainab ta mike, "Ina zuwa Hannatu, idan ban
dauko masa alewar nan ba ba zai bar mutane su
ji kumai ba."
Cikin sauri ta shige dakin nata da ke manne jikin
falon don gudun kar ta bata wa Hannatu lokaci.
Jim kadan ta fito alewar rike a hannunta. To
amma wani abin mamaki wanda ita kanta ta rasa
sanin dalilinsa shi ne, tun daga lokacin da ta
mike da zummar dauko Alewar sai ta ji zuciyarta
ta na bugawa kamar za ta faso kirjinta ta fito,
kuma har zuwa yanzu da ta shigo falon gaban
nata bai daina faduwa ba.
Tun kafin ta isa gare shi, Mujahid ya tafi da sauri
ya karbi alewar, sannan ya koma wajen mahaifin
nasa.
"Baba ka ga alewar!" ya ce ya na nuna masa.
"Na gani Mujahid, amma za ka sanwa su
Hauwa'u ko?"
Ya girgiza kai, "Ba zan ba su ba."
"Kannan naka?" A wannan karon aminin Alhaji
Basirun ne ya yi magana, wato Alhaji Gali.
"Ni dai ba kannena ba ne." Mujahid ya ce ya na
kumbura baki.
"To shi kenan rabu da shi, idan na je na dawo ba
zan kawo masa jirgi da mota ba." Cewar Alhaji
Basiru.
Alhaji Basiru mutum ne mai son hada kan
'yayansa a koda yaushe. Shi ya sa idan daya
daga cikin su ya zo da wani abu matukar sauran
ba su da shi, to sai ya ba su. A yanzu ma haka
ce ta kansance don sai da ya lallabi Mujahid ya
ba shi alewar.
"Yauwa Mujahid, ka ga idan na je na dawo sai na
sayo ma wata." yace bayan ya karbi alewar. "Bari
na raba mu ku ko?" Mujahid da fuskarsa ke a
turbune ya gyada kai cikin rashin son rai.
Alhaji Basiru ya bare alewar sannan ya sa hakori
ya fasa ta gida uku.
"Fara zaba Mujahid." Ya ce bayan ya zube ta a
tafin hannunsa.
Mujahid ya dubi kason alewar cikin rainuwa da
ruwan ido, ya sa hannu ya dauki daya. A hankali
sai kuka ya kufce masa. Ba wani abu ne ya sa
shi kukan ba, sai dariyar da Hauwa'u da Sailubar
su ka shiga yi masa bayan sun dauki nasu kason.
Ya dube su daidai lokacin da su ka sa alewar a
baki su na yi masa gwalo. Da tsananin fushi ya
dubi tasa alewar sai ya fashe da kuka, a lokaci
guda kuma ya yi jifa da ita kai tsaye ya fice daga
falon a guje ya nufi inda Hajiya Rukayya ta ke
(Kitchen).
Barista Hannatu ta mike, "Lallai Mujahid akwai
rigima..Ni zan tafi." Zainab ma ta mike.
"To, Hannatu a sauka lafiya, sai an kwana biyu
ko?" Alhaji Basiru ya mike.
"A gaida gida." Alhaji Sambo da Alhaji Gali su ka
ambata.
Momi...momi, Baba..ya kwace mini Alewa...ta".
Wannan shi ne abin da Mujahid ya rika ambata
cikin kukan nasa har ya isa gare ta.
Ba ta fahimci abin da ya ke nufi ba saboda haka
ne ma ta daka masa tsawa gami da kai masa
hannu da zummar mangare shi.
Maimakon damuwa da abin da ta yi masa sai ya
ci gaba da cewa cikin kukan nasa, baya ya dan
matsa baya, "Ba Baba ba ne ya kwace
min...A...Alewata da ki..ka ba ni a
makaranta...ya ba su Hau...Hauwa'u.."
Sai yanzu ta fahimci abin da ya ke fada, ta kuma
gane. A firgice ta saki kwanon abincin da ke rike
a hannunta, abincin ya tarwatse a farfajiyar dakin
girkin. "Kar ku sha alewar nan ba ta da kyau...kar
ku
sha alewar nan ba ta da kyau...kar ku sha!"
Wannan shi ne abin da ke fita daga bakinta cikin
daga murya da kuruwa, kuma shi ne abin da ya
katse sallamar da kawayen biyu ke yi (Zainab da
Barista Hannatu) Wadanda ke tsaye a bakin kofar
falon. Cikin kin jinin rabuwa da juna kamar yadda
su ka saba.
Tafiyar ruwa ta so ta yi da su ba don sun ba ta
hanya ba. Shakka babu ta tsorata su ganin
shigarta falon kamar kibiya. To, amma duk
wannan mai sauki ne, tsoron nasu ya fi bayyana
karara lokacin da su ka rufa mata baya zuwa
cikin falon su ka iske, Sailuba da Hauwa'u da
Alhaji Basiru kwance a kasa su na murkususu!
Turus su ka yi su dukansu sa'ar da kwayar
idanunsu ta nuna mu su mummunan abin da ke
faruwa a falon, abin da ya haifar da wasu irin
alamu na rikitarwa da kaduwa lokaci guda a
fuskokinsu, musamman ma Hajiya Rukayya da
abin ya yi ma ta yawa, ga 'yaya ga miji, su na ta
faman juye-juye da kakarin neman taimako.
A ka ta dora hannuwanta biyu ta kwalla wani irin
ihu mai garwaye da kuka. Lokaci guda ta nufe su,
ta dire gwaiwoyinta biyu akan kilishin da ke
shimfide a falon, ta tallafo kan Sailuba, ta girgiza
ta, kana da sauri ta mayar da ita ta tallafo
Hauwa'u ta girgiza, a yanzu sun daina motsi,
jikinsu ya saki kamar matattu. Take ta kuma
kurma wani uban ihu cure da wani kuka mai
tsuma zuciya.
"Wayyo Allahna... 'yan biyu sun mutu."
Wannan ya sa Zainab ita ma da ke tsaye tare da
kawarta cikin rashin sanin abin yi ta isa ga Hajiya
Rukayya da ke kokarin faduwa ta dafe ta. Ba ta
da abin fada shi ya sa ta kasa cewa komai, a
lokaci guda kuma hawaye ya fara tsattsafowa
daga idanunta ganin yara biyu da ke kwance ko
motsa wa ba sa yi, bugu da kari ga mijinta na
juye-juye cikin wani irin nishi na ban tausayi.
Dabara ce ta fado ma ta, shi ya sa ita ma Barista
Hannatu duk da cewa ta nacikin rikita ta motsa
zuwa inda Zainab ke rike da Hajiya Rukayya. Ta
duka da sauri ta tallafi Hajiya Rukayyar, "Sake ta
Zainb, je ki kira likitanku a waya mana."
Ba ta yi gardama ba kawai sai ta sakarwa
Hannatu ita, ta nufi kan wayar sadarwar da ke
ajiye kan matsakaicin teburin da ke durkushe can
gefe guda. cikin hanzari ta soma lallatsa
lambobin da su ne ta san za su sada ta da likita
Idris.
"Hello!" Ta ambata tun kafin ta gama daidaita
zaman wayar a kunnenta.
"Likita ne." Ta ci gaba.
"Don Allah ka yi maza-maza ka zo." Ta juya
kallonta ga maigidanta Alhaji Basiru jin ya ja wani
dogon numfashi.
"Likita ka yi sauri don Allah, alhaji ne da 'yan
biyu su ka kamu..." Aka katse ta daga can
bangaren ta hanyar ajiye wayar da likitan ya yi.
Ita ma ta ajiye, maimakon ta dawo gare su sai ta
nufi dakinta a guje, meyiwa akwai abin da ta
tuno.
Da sauri-sauri, gudu-gudu Zainab ta kuma
shigowa falon hannunta na dama rike da 'yar
karamar na'urar da likitoci ke rataya wa a wuya.
Wajen maigidanta ta fara nufa. Da gaggawa ta
balle maballen wuyan rigarsa ta dora na'urar a
kirjinsa bayan ta sakala a kunnuwanta.
To, a daidai lokacin ne Likita Idris ya shigo falon
da sauri, hannunsa rike da irin karamar jakar
nan
tasu ta likitoci.
Mamaki ne shi ma ya fara bayyana a fuskarsa
ganin abin da bai yi tsammani ba, Alhaji Basiru
kwance ya na nannauyan nishi.
"Subhanallahi." Ya ce. Har ya nufi Alhajin amma
ganin Zainab na yin iya bakin kokarinta, ya sa ya
sauya nufin nasa ya nufi su Sailuba da ko motsi
ba sa yi. Koda Hajiyya Rukayya ta kyalla idanu ta
ga Likita sai ta yi zumbur ta kwace daga hannun
Hannatu, ta mike ta tare shi ta nacewa, "Likita
don Allah taimake ni, wadannan 'yayan sun
mutu...wayyooo!" kukan ya hana ta ci gaba.
Cikin hanzari Likita ya dire yar jakarsa a kasa, shi
ma dai da yar na'urar da ke rataye a wuyansa ya
soma. Falon ya yi tsit sai nishin kukan Hajiya
Rukayya sakamakon zubawa Zainab da likita Idris
idanu da aka yi akan gwaje-gwajen da su ke yi.
Jim kadan likita Idris ya nisa, kana ya cira kai ya
dubi su Alhaji Sambo da ke cikin wani mugun ya
nayi,
"Wannan ya na da kyau mu tafi da su asibiti da
gaggawa domin..."
"To, mu je mana likita?" Kusan mutum uku ne su
ka katse shi (Ahaji Sambo da Alhaji Gali da Hajiya
Rukayya).
Ba su bata lokaci ba bayan umarnin likitan. Alhaji
Sambo da Alhaji Gali su ka tallafi Alhaji Basiru a
kafadarsu, su ka nufi waje da shi. Shi kuwa likita
Idris ya sungumi Hauwa'u, Barista Hannatu ta
sabi Sailuba Hajiya Rukayya ta sabi jakar likita
ita da Zainab su ka dafa mu su baya har zuwa
'yar farfajiyar da aka 'kirkira don ajiyar motoci.
Suna isa asibiti su ka zarce bangaren da ke da
alhakin bayar da tallafin gaggawa A&E (Accident
and Emergency). Sun amsa sunansu, domin ba
tare da jinkiri ba su ka fara aiwatar da tallafin
nasu na gaggawa akan Alhaji Basiru da 'yan biyu.
Bayan wasu 'yan gwaje-gwaje sai wata kakkaurar
likita fara, gajera, mai yalwar kumatu ta bayar da
umarnin a shigar da su wani daki. Amma a duk
cikin tawagar da su ka taho babu wanda aka bari
ya shiga. Hakan ne ya sa su ka koma gefe su ka
yi cirko-cirko su na jiran sakamako.
A CAN GIDA
***
Bayan fitar su da a kalla rabin sa'a Baraka ta isa
gidan a kudurinta na jin sakamakon abin da su
ka
kulla.
A bude ta samu babbar kofar shiga gidan,
wanda
hakan ne ya sa ta kunna kai ciki ba tare da
jinkiri
ba.
Ta ja ta tsaya ganin mujahid na ta rusa kuka,
mai gadi Bukar na ta rarrashin sa. Ga
mamakinta
sai ta ji gabanta ya yi mummunar faduwa. Ta
taka a hankali ta isa gare su.
"Assalamu alaikum." Ta ce a sanyaye.
"Wa'alaikis salam". Maigadi Bukar ya amsa, ya
cira kai ya dube ta.
"Sannu Baba." Ta kuma cewa a sanyaye.
"Yauwa ke ma Sannu." ya maida hankalinsa
gare
ta saboda sassauta kukan da Mujahid ya yi.
Ta yi murmushin karfin hali, "Lafiya dai ya ke
kuka?"
ya dubi Mujahid din da ke zaune kusa da shi
akan dogon bencin, "E to! Ba lafiya ba."
"Mene ne ya faru?" Ta bukata wannan karon a
'kagauce.
"Yan uwansa ne da kuma Alhaji ba su da lafiya."
"Su wa kenan?" Ta dafe kirji.
"Yan biyu mana, Hauwa'u da Sailuba."
Gabanta ya kara faduwa, "Me ya same su?"
"Abin da ban sani ba kenan. Ni ma ina zaune a
nan na ga an fito da su za a kai su asibiti."
Ba ta ga ta jira ba, akwai bukatar ta san dalili.
Ta matsa ta dafa kan Mujahid, ta rankwafa,
"Mujahid me ya same su?"
Cikin ragowar shisshikar kukan da ya ke yi ya
ce,
"Ba...alewa ta su ka kwace min...ba, shi ne..."
Ta
saki kansa da sauri wanda hakan ne ya hana shi
karasawa. Alamun razana su ka bayyana a
fuskarta, take ta ji cikinta ya juya gami da bayar
da wani amo kululululuuu, sai kuma ta ji kamar
ta saki gudawa, cikin ta yan maza ta ce, "Yanzu
su na asibitin?"
"Eh". Maigadi Bukar ya amsa ma ta kai tsaye.
"Wanne kenan?" Ta kuma bukata.
"Ai ina jin ba za su wuce asibitin nan na dogon
gida ba"
"Har Hajiya Raukayyar?"
"Dukan su!"
Ba ta sake komawa ta kansu ba ta juya, "Sai an
jimanku." Ta nufi babbar kofar da sauri da sauri
kamar za ta fadi. Idan ka dubi saurin da ta ke
yi
sai ka rantse da Allah asibitin ta nufa. Ko kusa
ba haka ba ne, ita Allah-Allah ta ke yi ta isa
gidan da ta sauka domin tattare kayanta ta nufi
tashar mota, don tuni ta kudurce ta kuma
gaskata kwanan Kano a yau ya gagare ta, yau a
kauyensu za ta kwana.
To sai dai abin da ba ta sani ba shi ne; Ko da
birnin Sin za ta koma bincike zai tuso keyarta
zuwa Kano.
***
Sa'a guda su ka share su na zaune su na jira
amma shiru ba labari, hakan ne ya kara jefa
zulumi a zukatansu, musamman Hajiya Rukayya
da ta riga ta san makasudin faruwar abin da
kuma irin hadarinsa. Duk ta rude ta kasa zaune
ta kasa tsaye, ta yi nan, ta yi can, ta na yi ta na
sumbatu. Abu guda ta ke nanatawa.
"Oooh! Wayyo Allahna, yau na shiga uku na
lalace...shi kenan mutuwa za su yi. Wayyo ni
kaina. Baraka ya haka?"
duk da cewa a rikice ta ke yin maganar, babban
abin mamaki da tambaya cikin abin da ta ke
ambata, me ya sa ta ke cewa shi kenan sun
mutu? Kuma wace ce Baraka? Wadannan
tambayoyi guda biyu su na yin matukar tasiri a
zukatan, Alhaji Sambo, Alhaji Gali da kuma
Barista Hannatu, sai kuma yan tsirarun mutanen
da ke zaune a wajen su na cikin jiran na su
majinyatan da su ka kawo.
A cikin wannan hali ne kofar dakin ta bude,
likitoci guda biyu su ka fito. Likita Idris ne da
wannan kakkaurar Likitar wadda ke amsa Dokta
Safina A. Bashir.
Cikin hanzari da kaguwa dukan su su ka tunkari
likitocin don jin halin da ake ciki.
"Ya ya likita...ya aka yi?"
"Ya ya su ke?"
"A wane hali su ke?"
"Me ya faru da su?" Ba za ka iya tantance
wadanda su ka furta wadannan kalamai ba a
cikin su, da ya ke kusan a tare su ka furta.
Bai ba su amsa ba sai kawai wani farin kyalle da
ya zaro daga aljihunsa ya tsane gumin da ke
tsattsafo wa daga goshinsa. Alama kawai ya yi
mu su da hannu su biyo shi. Su ka bi shi kuwa
duuu kamar kura har zuwa ofishinsa.
Kai tsaye likita Idris ya wuce ga kujerarsa da ta
sa wani madaidaicin teburin da ke dauke da
tulin
takardu.
Alhaji Gali da Alhaji Sambo su ka zauna a
kujerun
biyu da ke gefe da gefen madaidaicin teburin.
Barista Hannatu da Zainab da Hajiya Rukayya su
ka zauna a kan wata kujerar laushi da ke ajiye
gefe guda.
Likita Safina kuwa wucwe wa ta yi kusa da likita
Idris ta tsaya.
Bai bari shiru ta ratsa tsakanin zaman nasu ba,
likita Idris ya fara da cewa," ko da ya ke mun
bar
zane tun ran gini saboda dalilai na rikicewa,
ma'ana ba mu tambaye ku abin da su ka ci ya
kawo mu su wannan matsalar ba tun a lokacin
da na isa gidan dazu. To, amma duk da haka
zan
so sanin hakan yanzu, me su ka ci haka?"
Shiru ba wanda ya amsa tsawon dakiku goma,
kowannensu na kokarin tuno abin da ya san sun
ci, musamman ma Zainab da Barista Hannatu
da
su ka kasance a waje yayin Faruwar al'amarin.
Amma ita fa Hajiya
Rukayya ko shakka babu ta san abin da su ka
sha. Ta san alewa su ka sha, to sai dai ita ma
abin da ta ke tunani shi ne, shin wai maigidanta
shima Alewar ya sha? Alhaji Sambo ne ya kawar
da shirun wucin gadin da ya fara ratsa
tsakaninsu, bayan ya tuno abin da a iya saninsa
shi ne abin da ya gani sun sha a gabansa.
"Am...likita ni dai Alewa ce kawai na ga sun sha.
Amma fa shi Alhaji ban da shi domin shi kawai
dai ya raba Alewar ne da hakorinsa."
"Alewa?" Likita Idris ya maimaita cikin mamaki.
"Eh, Alewa." Alhaji Sambo ya tabbatar.
"Wacce irin Alewa?"
"Alewa dai da ka sani".
Likita Idris ya nisa, "To, tabbas wannan Alewar
akwai wata guba a cikinta, gubar da ke saurin
kashe Dan Adam. A ina aka samu wannan
Alewa?"
"A'a, mu dai ba mu sani ba, yaron nan mujahid
ne da ya ce ya na da Alewa da aka saya masa a
makaranta da safe. Ganin zai yi rikici sai Alhaji
ya sa mahaifiyarsa ta je ta dauko masa...ka ji
yadda aka samu Alewar?
Dasss! Kirjin Hajiya Rukayya ya buga. Yau shi
kenan asirinta ya tonu. Da wanne za ta ji?
Rashin lafiyar 'yayanta da maigidanta ko fallasa.
Nan da nan sai ya nayi na nadama ya fara kore
na damuwar da ke fuskarta.
"Wace ce ta dauko Alewar?" Likita ya bukata.
"Ni ce Likita". Zainab ta amsa kai tsaye
"A ina ki ka saya masa ita?"
"A'a, ba ni na saya masa ba...ina jin Hajiya ce ta
saya masa lokacin da ta kai su makaranta,
tunda..."
"Wacce Hajiya...Ni?!" Hajiya Rukayya ta yi
zumbur ta mike tsaye gami da dafe kirji.
Babu shakka yanzu ne ya kamata ta kare kanta
domin idan wannan damar ta wuce ta, to fa
babu
wata da za ta yi amfani da ita don yiwa kanta
garkuwa.
"Sam! Ni ba ni ba shi wannan shegiyar Alewar
ba."
Ta ci gaba cikin tsagalgalewa, "Ki nemi wanda ya
ba shi tun dare bai yi miki ba. Ni da ba na ma
falon ki ka dauko..."
"Kin ga saurara Hajiya, Zauna." A wannan karon
likita Safina ce ta katse ta, kana ta ci gaba, "Shi
dai wannan al'amari koma dai ya ya ke wannan
alewar ce ta zama sanadiyar mutuwar yan biyu
da kuma sa Alhaji cikin halin kaka-na-ka-yi,
halin
mutuwa ko yau ko gobe..." Maganar likita Safina
ta katse ganin dukkansu sun mike a firgice.
"La'ilaha illalLahu". Hajiya Rukayya ta fada cikin
daga murya, "Wayyo Allah...na ga ta kaina yau."
yanzu ne ya kamata ta yi amfani da abin da
zuciyarta ta kitsa mata. Nan da nan ta juya cikin
rufewar idanu ta cakumi wuyan Zainab, cikin
kukan ta ci gaba da cewa, "Ke munafuka,
wallahi
yau sai kin sanar da ni inda ki ka samu wannan
Alewar ki ka kashe min 'yaya na da mijina, sai
kin fada min...sai kin fada min!"
Ta na yi ta na jijjiga ta.
Barista Hannatu da Likita Safina su ka zaburo su
ka rike hannun Hajiya Rukayya da ta shake
wuyan Zainab. Da gumi da sidin goshi su ka
bambare hannun.
"Ni wallahi yau ba zan yarda ba...wallahi ba zan
taba yarda ba, shegiya, tsinanniya, da ma ki na
jin haushin yayan nan..." Ta kuma fashewa da
kuka.
Likita Idris ya mike daga kan kujerarsa, "kin ga
Safina, ku je waje da ita." ya yi Umarni.
Likita Safina da Barista Hannatu su ka janye
Hajiya Rukayya su ka fice daga ofishin su na
bata
hakuri.
Zainab kuwa tuni jikinta ya yi likis tana tsaye
dafe da wuyanta ta na wani irin dan tari, da
alama shakar da Hajiya Rukayya ta yi mata ta
kai matuka saboda idanunta sun kada sun yi
jajur.
Yanzu ofishin ya yi shiru kamar ruwa ya shanye
su, meyiwa maganganun da Hajiya Rukayya ta yi
ne sunyi tasiri a zukatansu Don kuwa tuni wasu
daga cikinsu sun shiga zargin Zainab din a
matsayin ita ta sa guba a cikin muguwar Alewar.
Likita idris ya nisa cikin rashin sanin abinyi,
Hakika shi ma yan surutan da Hajiya Rukayyar
ta
yi yasa zuciyarsa ta fi karkata ga darasin da ke
nuni da cewa Zainab ce ta samar da wannan
Alewa, kuma yana zargin tayi haka ne ga hajiya
Rukayya domin ta hallaka ta da yayanta.
Ya dubi Zainab a sanyaye yace "Hajiya Zainab".
ya nuna mata gun zama. Zainab ta zauna a
sanyaye hannunta rike da wuyanta.
"Alhaji". Likita Sambo ya ambata ya na duban su
Alhaji Sambo da su ke zaune cikin mutuwar jiki.
Su ka cira kai a hankali su ka dube shi. Babu
wanda ya samu amsawa.
"Ko da ya ke". Likita ya ci gaba, "Zainab ku ya
kamata na tambaya."
Ta cira kai a hankali ta dube shi.
"Tsakani da Allah Zainab a ina kika samu
wannan
Alewar. Ki daure ki sanar da mu sai mu je har
gurin domin daukar mataki ga mai sayarwar. Ta
yiwu ke ba ki san mai guba ba ce."
Zainab ta sa mayafinta ta goge hawayen da ke
faman bulbulowa daga idanunta. Abin gwanin
ban
tausayi, ta soma magana, "Likita, na rantse da
Allah ba ni na saya masa wannan Alewar ba,
hasali ma ni ban san da ita ba sai a lokacin da
aka ce na dauko. Wallahi...walla..." kukan da ta
soma ya ci karfinta ya hana ta karasawa.
"Kin ga malama saurara, babu wani kukan
munafurci da za ki yi mana, kawai ki sanar da
mu inda ki ka samu wannan guda." Alhaji
Sambo
ya ce da ita a kufule kuma cikin tsawa, don tuni
shi ya sakankance a zuciyarsa cewa ita ce ta
samar da Alewar, idan ba haka ba ai Hajiya
Rukayya ba za ta sayo abin da zai kashe ma ta
ya ya ba.
"Kawai abin da ya dace ki sanar da mu kenan
amma ba rantse-rantse da kukan munafurci
ba."
Shi ma Alhaji Gali ya dora cikin fushi.
Zainab ta ji kamar gini ya ruguzo ma ta a ka, jiri
mai tsananin gaske ya afka ma ta sakamakon
wadannan maganganun da ta ji daga bakin
mutanen da ba ta taba tsammanin za su zarge
ta
ba.
Nan da nan sai ta ji wata marainiyar murya
daga
can cikin Zuciyarta da ke iya sa mai sauraro
kuka
ta fara ambatar, "Wayyo Allahna, yau ya zan yi
da
kaina. Ubangiji ka kawo mini dauki cikin wannan
al'amari."
Likita Idris ya kuma nisawa. Yanzu kuma
hankalinsa ya fara rabuwa tsakanin yarda da
rashin ta da cewa Zainab ce ta samar da
Alewar,
a dan nazarin da ya yi wa fuskarta a yanzu.
"Hajiya." Ya kuma kiran sunanta.
Ta dago kai ta dubeshi, har yanzu ofishin juya
ma ta ya ke yi.
"Yanzu ke kin tabbatar ba ke ki ka samar da
wannan Ale..."
"Ka ga likita saurara! Ai sam babu bukatar ta
tabbatar tunda na fuskanci ba ta da shirin fadar
gaskiya. Mu da aka yi komai a gabanmu?" Alhaji
Sambo ya katse shi kana a na huci ya ci gaba,
"Ka rabu da ita kawai Likita, idan mu ta ki sanar
da mu ai ta sanar da hukuma ko?" Ya mike
tsaye,
"Tashi mu je Alhaji Gali."
Alhaji Gali ya mike. Har sun kai ga bakin kofar
fita daga ofishin, Alhaji Sambo ya juyo, "Za mu
je
ga jami'an tsaro Likita, don Allah ku ba Alhaji
Kyakkyawar kulawa, yanzu za mu dawo."
***
Karfe Bakwai saura minti biyar su ka isa babbar
Hedikwatar yan sanda kamar yadda agogon da
ke
like a gaban motar ya nunawa kwayoyin idanun
magidantan biyu (Alhaji Sambo da Alhaji Gali)
wadanda su ka zo don kawo karar Zainab a
matsayin matar da ta aikata kisan kai.
Bayan samar wa motar kyakkyawan matsuguni
cikin yalwatacciyar harabar ginin Hedikwatar, su
ka bude motar su ka fito, a lokaci guda su ka
mayar da murafen su ka rufe. Kallo daya za ka
yi
wa fuskokinsu ka tabbatar akwai gagarumar
matsala da ke damun su.
Kamar kurame su ka dubi junansu ba tare da
sun
yi magana ba, su ka tunkari wata yar majalisa
da
wasu yan sanda biyar su ka kafa, su na hira,
meyiwa su na yi wa juna murnar busharar da
shugaban kasa ya yi mu su ne akan karin
albashi.
Sa'ar da su ka isa ga yan sandan su ka yi mu su
sallama duk sai su ka juyo gami da amsawa.
"Sannun ku." Cewar Alhaji Gali.
"Yauwa, Alhaji ya gari?" Cewar biyu daga cikin
yansandan.
"Ma su gidana don Allah mu na neman ofishin
bincike ne game da kisan kai."
"Ofishin ASP Haladu kenan ko?" Daya daga cikin
yansandan ya bukata ga yan uwansa.
"Eh, nan ne." Yan sandan su ka tabbatar ma sa.
"Ya na cikin gidan nan kuwa? Anya bai fita ba?"
Dan sandan ya bukata bayan ya dubi fuskar
agogon da ke daure a hannunsa, "Yanzu fa
karfe
bakwai saura minti uku."
"Kai ya na nan bai fita ba, ba ga motarsa can
ba." Daya daga cikin yan sandan ya amsawa dan
uwansa bayan ya kai dubansa ga tsiraran
motocin da su ka sage a harabar.
"Eh, kwarai bai fita ba." Dan sandan ya amsa,
"Ku
zo mu je mu je na raka ku." ya ce da su Alhaji
Gali. Ya juya su ka ki shi a baya, su ka ratsa ta
tsakanin wasu yan furanni da aka jera gefe da
gefen yar siririyar hanyar da za ta sada mutum
da makeken benen.
Daraf-Daraf su ka haye, su ka nufi wani lungu.
A
can kuryar lungun ofishin ya ke. Manne a bango
jikin wani katako da ke saman kofar ofishin
kadan, an rubuta cikin manyan haruffa
"HOMICIDE"
kasancewar a bude su ka same shi ba su yi
jinkiri
wajen kunna kai ciki ba. Faffadan ofis ne kuma
ciki da falo.
A zaune su ka iske wani Dan sanda mai
mukamin
sajen (Igiya Uku) ya sanya dan madaidaicin
tebur
a gaba ya na ta faman rubuce-rubuce.
"Wa'alaikumus salam." sajen Sani ya amsa
sallamar mutanen uku bayan ya cira kai daga
rubutun zuwa duban su.
"Ah! Auwal ya aka yi?" ya mika wa kofur Auwal
hannu. (Dan sandan da ya rako su alhaji sambo)
.
Su ma su Alhaji Gali su ka mika masa Hannu, su
ka gaisa.
"Don Allah ko mai gida na ciki?" Cewar kofur
Auwal.
"Ya na nan" Sajen Sani ya amsa kai tsaye.
"Yauwa, dama wadannan bayin Allah ne ke son
ganinsa"
sajen Sani ya dubi agogon da ke daure a
hannunsa.
"Kai karfe bakwai fa yanzu, kai ma ka san ganin
maigida ba zai yi wuya a yanzu. Sa'a aka yi fa
yau mu na son kawo karshen wani bincikenmu
akan wani kes (Case) da za a shiga kotu gobe,
idan banda haka ai karfe uku mu ke tashi"
"Gaskiya da farko ni ma na dauka kun tashi"
cewar kofur Auwal. Ya juya ga su Alhaji Gali
"Alhaji Me zai hana gobe ku dawo da wuri ku
gan
shi, kun ga yanzu dare ya kawo kai.."
"Don Allah yallabai a taimaka mana mu gana da
shi yanzu, wani gagarumin al'amari ne..wata
mata ce ta kashe yayan kishiyarta biyu da kuma
jefa mijinta cikin gagarumin hadari. Don Allah a
taimaka kar kafin goben ta gudu" Alhaji Sambo
ya
ce a sanyaye cikin muryar roko.
Idannun yansandan ne su ka kara girma
(alamun
mamaki da tsoro) Hakika babban kes ne, ya
kamata su bi diddiginsa.
Sajen Sani ya rufe littafin da ya ke rubuta a ciki
ya mike tsaye da gaggawa, "Ina zuwa" ya ce
kana ya nufi kofar da ke like cikin ofishin nasa
wadda kuma ita za ta sada shi da maigidan
nasa
ASP Haladu. Ya turo kofar ya rufe bayan ya
shiga. Ya kame ga mutumin da ke zaune kan
wata babbatar kujerar laushi, damfareren
teburin
da ke take da takardu durkushe a gabansa.
"Sani ya ya?" ASP Haladu ya bukata.
Ya saki jikinsa daga kamewar da ya yi, "Yallabai
wasu ne dauke da wani muhimmin kes, su ke
son
ganin ka" "Yanzu abin da na ke so da ku." ya
mayar da
dubansa gare su, "Ku tashi maza ku koma
asibitin, ku tattara kawunanku gaba daya ku
hallara a gidan, don nan da karfe takwas zuwa
tara za mu zo domin yin bincike."
Ya dubi agogon da ke rataye jikin bangon
ofishinsa,
"Kun ga yanzu bakwai har da kwata."
"To yallabai." su ka amsa kusan a tare."
"Har fa gawar yaran mu ke so a mayar gidan.
Ku
yi maza don Allah." ya rufe littafin da ke
gabansa.
"An gama yallabai." Su ka kuma ambata, kana
su
ka nufi kofar fita.
Su na fita ya janyo wayar sadarwar da ke dare a
kan teburin ya soma laluban lambobi cikin sauri.
***
Tunda Motar yansandan da ke dauke da
yansanda hudu ta shiga faffadar unguwar, Sifeto
Habibu da ke zaune a kujerar gaban motar ya
ke
ta rarraba idanu cikin fatan ganin lamabar da
aka
ba shi wadda aka ce ita ce lambar gidan Alhaji
Basiru. Abinka da unguwar masu hannu da
shuni,
shiru babu motsin komai sai haushin karnuka da
ke tashi lokaci-lokaci.
"Tsaya mun zo gidan." ya ce ya na duban
Direban bayan ganin lambar da maigidansa ASP
Haladu ya ba shi sakale jikin kofar gidan da su
ke
kokarin giftawa.
"No 20 B KNS." ya kuma ambatar lambar a fili,
ya
na duban wadda ya rubuta jikin wani dan littafi
da ke rike a hannunsa, a lokaci guda kuma ya
na
duban wadda ke makale jikin kofar. Tabbas
yanzu
ya yarda gidan ne, don haka sai ya umarci
Direban da ya gyara tsayuwar motar a gaba da
gidan kadan.
Ba gaba dayansu ne ba ne sanye da kayan aiki
a
jikinsu. Su ka mayar da murafen motar su ka
rufe. Sifeto Habibu ya jagorance su har bakin
makekiyar kofar. Sau daya kawai ya kwankwasa
kofar, jim kadan sai su ka ga ta bude. Ba su yi
mamakin hakan ba don sun san an san da
zuwansu.
Maigadi Bukar ne ya bude kofar.
"Sannunku da zuwa." Ya ce da alamun mamaki
a
fuskarsa. Meyiwa saboda ganin su da ya yi ba
yadda ya zata ba, cikin fararen kaya, "Ince dai
ko
kune jami'an tsaron".
"Eh, mune Baba". Daya daga cikin su ya bashi
amsa a takaice.
"Bari nayi muku jagora zuwa ciki".
"To, Baba." Sifeto Habibu ya amsa. Har maigadi
Bukar ya shiga gaba da zummar su bi shi zuwa
ciki, sai Sifeto Habibu ya ce, "Baba kafin mu
shiga ciki ina so na yi ma wasu yan tambayoyi a
matsayinka na maigadin wannan gida."
Maigadi Bukar ya tsaya, "To, Dan nan, Allah ya
sa na sani."
Sifeto ya yi murmushi, "Ai sanannen abu ne a
gare ka domin kuwa adadin shekarun da ka
kwashe kana aiki a wannan gida na ke so mu
sani."
"E to! Ku san ni ne maigadi na farko tun gina
gidan."
"kusan ne, ko kuma kai ne?" Sifeto Habibu ya
nemi tabbaci.
"To, ni ne".
"To Baba da ya ke kai ne maigadi tun farko, ko
ka san wani abu game da Alhaji da matansa?"
Shiru tsawon dakiku bai amsa ba, can ya nisa,
"Yallabai ka san tsakanin miji da mata sai Allah,
gaskiya ni kullum ina nan bakin kofa, zai yi wuya
na san abin da ke gudana a ciki, sai dai kawai
na
san kirki da rashin kirkin kowacce a cikin matan.
Idan shi ka tambaye ni zan iya fada ma. Tunda
mai kyauta da mai rowa ma Allah Bai yi su
daidai
ba."
Kusan dukansu sai da su ka yi murmushi.
"Banda wannan Baba." Sifeto Habibu ya ce, "To,
bayan kai akwai wani ma'aikaci a gidan?"
"Eh, kwarai kuwa, akwai abokin aiki na amma
shi
ya jima da rasuwa, don yau..." ya cira kai sama
alamar tunani, "Ina ga zai kai shekaru kamar
bakwai da rasuwa."
A wannan karon kusan ya ba duk yan sandan
haushi,
musamman Sifeto Habibu da shi ya ke
tambayoyi.
"Banda wanda ya rasu Baba. Bayan wannan ba
wanda ya ke aiki a gidan ko da ba irin naka
ba?"
"Eh, lallai akwai Lukman, amma shi Direba ne."
Sifeto ya gyada kai, "Ko ya na nan yanzu?"
"A'ah ba ya nan, don shi rabonsa da gidan nan
tun da rana da ya dauko yara daga makaranta,
kuma shi da ma haka al'adarsa ta ke, idan ya
kai
yara makaranta ya koma da rana ya dauko su
to
aikinsa ya kare sai kuma gobe.
Shi ya sa ko dazu ma da za a kai su Alhaji asibiti
sai wata Bakuwar Hajiya Karama (Zainab ya ke
nufi) da kuma kanin Alhaji ne su ka ja motocin"
Sifeto Habibu ya nisa gami da gyada kai alamar
gamsuwa, "Wato yanzu kai kana nufin shi
Lukman ba ya nan abin ya faru?"
"Sosai" In ji maigadi Bukar.
"To Baba na ji kuma kawar Hajiya Karama, wace
ce Hajiya Karama?"
"Amaryar Alhaji Kenan" Ya amsa cikin dariya,
"Ita
a ke cewa Hajiya Karama, amma ni kadai na ke
fada mata saboda la'akarina na ga cewa ita ta
zo
gidan daga baya"
"To, ita wannan kawa ta Hajiya Karama ko.."
"Ba fa sunanta Hajiya Karama ba, ni kadai na ke
fada mata. Sunanta Zainab" Maigadi Bukar ya
katse Sifeto Habibu.
Sifeto Habibu ya yi dariya, "To, ita kawar ta
Zainab ya sunanta?"
"In ga?" Ya yi jim, "Sunanta Hannatu"
"Kar dai ka gaji Baba, kasan aikin da mu ka zo
yi
kenan, ko za ka iya tuno tsawon lokacin da ita
Hannatun ta dauka a cikin gidan, ma'ana tun
yaushe ta zo, kuma yaushe ta fita?"
"A'a dama ita al'adarta tunda na san ta, idan ta
zo tun safe ba ta barin gidan nan sai yamma
likis. To yau din ma ina zaune anan daidai
lokacin
da ta saba tafiya sai na ga sun fito gaba daya
cikin halin rikita. To! Ka ji." Kusan gaba daya
duk wanda ya kasance a falon
yayin da al'amarin ya faru dazu, ya na cikin
falon
yanzu idan ka duke Barista Hannatu da kafin su
Alhaji Sambo su koma asibitin ta tafi gida, sai
kuma Hajiya Rukayya da ke can dakinta a
kwance
kasancewar ciwo da ta ce kanta na yi.
Bayan yan gaishe-gaishe da jajantawa da yan
sandan su ka yi ga mutanen da su ka iske a
falon
sai jagoran tafiyar, Sifeto Habaibu ya bukaci
ganin gawarwakin su Hauwa'u.
Ba tare da bata lokaci ba, Alhaji Sambo da Alhaji
Gali su ka kai yan sandan wani daki da ke like
cikin falon inda anan ne su ka shimfidar da
gawarwakin. Lillibe da farin kyalle su ka iske su.
Sifeto Habibu ya isa gare su ya duka a hankali
ya
yaye kyallen iya fuskokinsu. Idanunsu duk a rufe
su ke. A hankali ya mayar ya rufe kana ya mike
ya dubi jama'ar tasa.
"Doctor Nasir." Ya kira sunan daya daga cikin su.
"Na'am yallabai." wani dan dogo ya amsa.
"Ina so ka yi mana kyakkyawan bincike akan
wadannan." ya nuna gawarwakin, "Mu za mu
koma falon."
"An gama yallabai." ya ware daga cikin yan
uwansa ya nufi gawarwakin, daidai lokacin da su
Sifeto Habibu da sauran yan sandan su ka fice
daga dakin zuwa falon.
Har yanzu Zainab da ke zaune kan daya daga
cikin kujerun falon na nan, ta zabga tagumi,
hawaye sai kwaranya ya ke daga idanunta,
danta
Mujahid zaune kusa da ita, shi ma ya na kuka,
meyiwa saboda ya ga ta nayi.
Bayan sun kuma zama sai Sifeto Habibu ya dubi
Alhaji Sambo, "Alhaji da ya ke kai ne kanin
maigidan nan uwa daya uba daya, ko za ka iya
sanar da mu iya adadin yan uwansa bayan kai?"
ya girgiza kai, "Babu yallabai, mu biyu ne kawai
a
wajen iyayenmu."
"To, su iyayen naku su na nan a raye?"
"A'a, sun jima da rasuwa, don ni ban ma san su
ba, tun ina karami su ka yi hadarin mota su ka
rasu."
Sifeto Habibu ya gyada kai, "To, bayan wannan
ko ka san wani mutum da su ke muhimmiyar
alaka da shi."
"Su na da yawa, ga daya ma kusa da ni. Shi ne
ma babba daga cikin aminansa." Ya nuna Alhaji
Gali. Shi kuwa ya yi dan Murmushi.
Sifeto ya kalle shi, "Alhaji kasancewarka aminin
Alhaji fiye da kowa cikin aminansa, bai taba
sanar
da kai cewa akwai wani abu da ke damun sa ba,
kafin wannan abin ya faru da shi?"
ya girgiza kai, "Bai taba ba, sai dai kawai
matsaloli na gida da ya ke yawan kawo min, ina
nufin game da iyalansa."
"Matansa kenan?" Bukata daga Sifeto Habibu.
"Eh." Amsa daga Alhaji Gali.
"Kamar wace irin matsala ya ke yawan kawo ma
game da su?"
"Rashin zaman Lafiya a tsakaninsu."
"Kamar ya ya?" Sifeto ya bukata bayan ya ware
hannuwa.
Sai da ya yi gyaran murya domin bai yi
tsammanin Sifeto zai nemi sanin irin matsalar
ba.
"Kamar yawan rikici da su ke..."
"Na gane wannan." Sifeto Ya katse shi, "Game
da
me su ke yin rikicin?"
Alhaji Gali ya dubi Zainab, "Kamar ita amarya
da
ta ke shan tsangwama da matsi daga uwar
gidan..."
"wato dai ka na so ka ce uwar gidan ce ke
haifar
da matsalar."
"Eh, haka ne."
Sifeto ya gyada kai bayan ya dubi dan sandan
da
ke ta faman rubuce-rubuce. Ya mayar da
dubansa ga Zainab da har yanzu ke ta faman
zubar da hawaye. Ba wani abu ne ya sa ta cikin
wannan ya nayin ba sai sharrin da aka kulla
mata, ita a rayuwar duniya ba abin da ta tsana
irin a ce ta yi abin da ba ta yi ba.
"Wannan wacce ce daga ciki?" Sifeto ya nuna
Zainab.
"Ita ce Zainab, amaryar kenan". Alhaji Sambo ya
amsa.
"Sannu amarya." sifeto Habibu ya ce da ita, "Ya
mu ka kara ji da hakuri."
"Hakuri sai Ma'aiki." Ta amsa da kyar cikin
muryar kuka.
"Hajiya, mu ma'aikata ne kamar yadad ki ka
sani,
mun zo ne domin warware wannan dambarwa
musamman ma ga ke da ake zargi a matsayin
matar da ta aikata kisan kai..."
Zainab ta girgiza kai, "Wallahi Yallabai ba ni ba
ce hasalima ni ban san da wata Alewa ba sai da
aka umarce ni na dauko." Ta fashe da kuka.
"Ya isa Hajiya." Sifeto Habibu ya dakatar da ita
ganin kukan na kokarin tsawaita, "Ba kuka za ki
yi ba. Abin da kawai na ke so ki gane shi ne,
hukuma ba ta yankewa mai laifi hukunci har sai
ta yi bincike ta tabbatar da laifinsa. To daga nan
kuma sai ta hukunta shi daidai da abin da doka
ta shimfida." ya tsagaita, kana ya ci gaba ganin
ta sassauta da kukan, "Hajiya kin ce ba ki san
da
wannan Alewar ba a farko har sai lokacin da aka
umarce ki da ki dauko ko? Ta gyada kai.
"To, wane ne ya umarce ki ki dauko?"
"Alhaji ne."
"Alhaji? Maigidanku kenan?"
"Eh."
"To shi ya aka yi ya san da Alewar?"
ta yi shiru na dan lokaci kana ta ce, "Shi ma bai
san da ita ba sai bayan da mujahid ya ce ya na
da ita a aljihun wandonsa na makaranta."
"Wto ya tabbata ke ki ka je da hannunki ki ka
dauko Alewar ki ka kawo ko?"
"E, ni na dauko."
"Ya gyada kai," To, wane ne Mujahid."
"Ga shi." Ta dafa kan Mujahid da ke zune kusa
da ita shi ne dan naki?"
"shi ne." Ta tabbatar.
"Zo Mujahid." Sifeto ya ce ya na dubansa gami
da mika masa hannu.
"Tashi ka je". Zainab ta ce da shi ganuin ya na
dubanta.
Mujahid ya mike idanunsa fal da kwalla ya nufi
Sifeto, tun kafin ya kai gare shi ya mika hannu
ya
rike shi.
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
Bakin Kishi 3
Posted by ANaM Dorayi on 08:22 AM, 29-May-15
"Yaro kai ne Mujahid?"
"Uhm!" ya amsa a ciki gami da gyada kai, a
lokaci guda kuma ya na waiwayen mahaifiyarsa.
"Wace ce mamanka?"
ya nuna Zainab.
"Ka na makaranta?"
"E, ina yi." A wannan karon ya bude baki.
"A wacce makaranta ka ke?"
"Sasif Model School".
"Ajinka nawa?"
"A Naziru tu (Nursery 2) na ke." Mujahid ya
amsa.
Lallai yanzu ya tabbatar mujahid ya na da wayo.
To amma ya na so ya tabbatar saboda tambayar
da ya ke son yi masa sai mai wayo sosai ne zai
iya amsawa.
"Ka iya turanci?" Ya bukata bayan ya saki
murmushi.
Ya gyada kai, "E, na iya".
"Idan na yi maka tambaya za ka iya mayar min?"
ya gayda kai ba tare da ya yi magana ba.
"How old are you?" (Shekarunka nawa).
"I am five years old." (Shekaruna biyar).
Kusan ba wanda bai ba sha'awa ba, saboda
yadda ya amsa turanci ba tare da rawar baki ba.
Yanzu Sifeto Habibu ya samu tabbacin Mujahid
na da wayo sosai, hakan ne ya ba shi damar
shiga yi wa Mujahid tambayoyi kai tsaye,
"Mujahid wane ne ya saya maka Alewa?"
"Momi babba ce."
"Wace ce Momi babba...wannan?" ya nuna
Zainab.
"A'a." Mujahid ya ce da girgiza kai, "Daya
Momin."
"Waccekenan?"
"Momin yan biyu."
Sifeto ya gyada kai, ya gane wadda Mujahid ya
ke nufi, "To, a ina ta saya ma?"
"A makaranta."
"Yaushe?"
"Un...un, gobe da safe."
"Gobe da safe? Ko dai yau da safe?" Sifeto
Habibu ya gyara masa. Ya san shirme ne na
yaro. Kuma ya kwana da sanin cewa ba kowane
yaro ne ke iya rike lissafin raneku ba.
"Eh, yau da safe ne." Mujahid ya gyara.
"A wajen Habu mai shago, na makarantarmu."
"Ka tabbatar?"
ya gyada kai.
Sifeto Habibu ya juya ga su Alhaji Sambo, "Alhaji
ina ita uwargidan ta ke, ko ta na asibitin?"
"A'a, ta na cikin daki, ba ta jin dadi ne."
"Assha! Allah ya sawake. A wane daki ta ke?"
"Ta na dakinta, zo mu je." Alhaji Sambo ya gayya
ce su bayan ya mike tsaye.
Yan sandan su ka mike su ka dafa masa baya,
su ka bar Alhaji Gali da Zainab da Mujahid a
falon.
Sa'ar da su ka isa dakin Hajiya Rukayya kwance
su ka same ta kan gado ta na ta faman barci,
amma na karya.
Kafin shigowarsu idanunta biyu, amma jin
motsinsu na nufo wa dakin ya sa ta rufe idanun
nata kamar mai barci.
A nata tunanin wannan wata hikima ce da za ta
kubutar da ita daga tuhumar yansandan, don
gudun kar a gane ita ce sanadin afkuwar aika-
aikar.
Su ka dan tsaya a kanta, tsayuwa ta yan dakiku.
Bayan kiran da Alhaji Sambo ya yi mata a kalla
sau biyar, shiru babu ko motsi, sai Sifeto Habibu
ya ce, "Kyale ta Alhaji mu koma falon."
Babu wanda ya yi magana su ka juya su ka fice
daga dakin.
Su na shigowa su ka iske Doctor Nasir zaune ya
na jiran su.
"Ya ya Doctor, me ka gano?" Cewar Sifeto
Habibu.
Doctor Nasir ya mike tsaye, "Yallabai binciken da
na yi na samu akwai guba mai hadarin gaske a
jikin Alewar da su ka sha, wanda gubar na iya
kashe mutum nan take.
Idan kuma wasu halittu ne ba mutum ba, ba sai
sun kai ga sha ba, ko shakar ta su ka yi za su
iya mutuwa."
Sifeto Habibu ya jinjina kai, "Yanzu dai ka gama
kenan?"
"E, na gama."
Sifeto ya juya ga su Alhaji Sambo, "To, Alhaji a
yanzu mun kammala wannan a matsayin rukuni
na farko kafin mu dawo na biyu. Kuma kamar
yadda doka ta tanada, za mu tafi da ita amaryar
har zuwa lokacin da za mu kammala bincikenmu
mu mika abin kotu."
Zainab ta cira kai da sauri ta dube shi, "Yallabai
me na yi?"
"Ana zargin ke ce da hannunki ki ka dauko alewar
da ta kashe wadannan yara."
Kasa magana ta yi, kawai ta kifa kai ta shiga yin
wani kuka na takaici, kukan da ka iya sa mai
dakakkiyar zuciya taya ta. Amma duk wannan bai
hana jami'an tsaron tafiya da ita ba, har da
Mujahid ganin ya ki yarda a tafi da ita a bar shi.
***
Kamar yadda ya zame masa sabo zuwa gidan
karfe bakwai na safe domin kai yara makaranta,
yau ma haka ne. To amma sabanin lokutan baya,
yau ya riski mummunan labari da bai taba
tsammani ba koda a mafarke-mafarken da ya sha
yi a daren jiya.
Tun da dai ya iso gidan ya ke zaune wajen
maigadi Bukar wanda ya labarta masa faruwar
mummunan abin, sai ya ji duk jikinsa ya mutu.
Ya cire tagumin da ya zabga hannu bibbiyu bayan
ya nisa, ya dubi maigadin,
"Wato yanzu kenan kana so ka ce yan sandan
sun gane cewa Zainab ce ta aikata laifin?"
"Ba ni ne na ke son na ce ba, hakan ne. To idan
ma ba haka ba, me ya sa su ka tafi da ita?"
Lukman ya jinjina kai, yayin da shi kuma Bukar
ya ci gaba da cewa.
"Kai lallai mugu ba shi da kama. Kaga dai matar
nan idan bangaren sakin fuska ne, kyauta da
alheri ba kamar ita, ashe ashe... Shi ya sa fa
wasu suke cewa mai shiru-shiru mugu ne, ko ni
yanzu da na auri ami shiru-shiru gwanda mai
suru..."
"Ba haka ba ne!" Lukman ya katse shi "Ni ina da
jan akan wannan al'amari, domin tabbas na san
Zainab ba zata aikata wannan danyen aikin ba."
"Uhm, uhm, Lukman.. Ka ga! Ka kiyayi kanka da
shisshigi cikin wannan magana domin kuwa abin
ya dangana da hukuma, idan aka ji kana fadar
haka kai ma za ta iya shafarka."
(Ayimin afuwa narasa kusan phragrap daya)
Ta yi shiru na dan lokaci, kana ta ce "Lukman-
Lukman na ji ka ce ka yi laifi da ka zo yau ko?"
"Cewa na yi, na yi ko ban yi ba?" ya gyara ma
ta.
"To ba ka yi ba, ai dama kwana daya mu ka yi
ko?"
"Eh." Ya gyada kai.
Falon ya yi shiru na dan lokaci.
"Lukman ina bukatar wani taimakone gare ka
kamar yadda ka yi min na baya..." A bazata ya
ji
maganar, har sai da ya dan zabura.
Ya kalle ta a bukace da son jin taimakon, "Hajiya
kamar na me fa?"
Maimakon ta fada masa, sai ta ce, "Lukman a
wancan karon nawa na ba ka?"
"Du...bu daya." Ya amsa cikin rawar baki a
tunaninsa cewa za ta yi ya biya ta.
"Yau na shigangada, ina zan samu dubu daya."
Ya ce a ransa.
"To, a wannan karon aikin da zan sa ka ya
rubanya na baya a kudi sau goma, kuma mafi
sauki wajen aiwatarwa akan na baya. Ka ga
kudin
zai kai dubu goma kenan."
"Dubu goma Hajiya?" Bai san sa'ar da ya ambaci
hakan ba.
A iya rayuwarsa yau shekaru arba'in da daya
kenan bai taba rike naira dubu goma tasa ba.
Koda ya ke ba anan ya fara aikin tuki ba, ya
fara
ne a gidan wani attajiri A.A. Boza. A wancan
lokacin ya dai sha ganin makudan kudi, ya ma
sha raka Alhajin banki karbo miliyoyi, amma duk
wannan ba ta sa ya taba rike dubu goma a
matsayin mallakar sa ba, har zuwa sa'ar da ya
bar gidan ya dawo nan.
"Eh, dubu goma Lukman, ka na ja ne?" Ta
tabbatar ma sa gami da bukata.
Ta ci gaba jin ya yi shiru "Me ka gani? Kawai
idan za ka iya ka amsa min, sai na baka rabin
kudinka tun yanzu ka ga zarar ka kammala sai
ka karbi rabin."
"To..to Haji..ya ya wanne irin aiki ne wan...nan?
Ke ba ki fada...min ba har yan...zu." Ya ce
bakinsa na rawa.
"Ba wani aiki ba ne magana ce kawai ta fatar
baki."
"Idanunsa suka kara girma (alamar mamaki).
Ya za a ce daga maganar baki mutum ya sami
dubu goma? "Shekara nawa dubunnai daga cikin
al'umma ke dauka su na aikin karfin
musamman
a wannan kasa tamu da mutum ke dama da
talauci amma su ke gaza mallakar dubu goma?"
a zuciyarsa ya fada.
"Ya ka ce?" Ta dawo da hankalinsa gare ta.
"Hajiya ina tunanin wacce irin magana ce
mutum
zai fada da baki kawai ya sami Naira dubu
goma?
Ta kyalkyale da dariyar karfin hali har da kyakya
cewa.
"Ka ga kuma magana ce mai sauki wajen fada,
kwatankwacin gyada kai ko girgizawa ga mutum
yayin da ya ke amsa tambayoyi, abin bukata
kawai, za ka iya?"
"Ka ce za ka iya dubu goma ba wasa ba ce."
Wani sashe a zuciyarsa ya rada masa. Kai tsaye
kuma ya ci gaba da lissafa ma sa abin da zai yi
da dubu gomar, ciki har da auren dalleliyar
bazawara sauta ga wawa.
"Eh..zan iya." Ya amsa kai tsaye.
Ta dan kau da murmushin da ke kan lebbanta.
"Ka san duk abin da ya faru a gidan nan ko?"
Ya jinjina kai. "Na sani Hajiya."
"To a takaice dai yan sanda jiya sun zo sun yi
bincike amma ni ba su bincike ni ba saboda ba
ni
da lafiya amma kowane lokaci daga yanzu su na
iya zuwa kuma dama wanda su ka rage ba a
yiwa tambayoyin ba mu biyu ne, ni da kai."
Ya yi zumbur ya mike tsaye cikin firgici, "To ni
me
na yi?" Ya bukata cikin saurin baki. A rayuwarsa
duk barikin da ya yi ya na karami ba abin da ya
fi
tsoro irin yansanda, duk da kasancewarsa gwani
kuma shugaban zuke-zuke da caca a kauyensu
wancan lokacin.
Ta bi shi da kallo cikin mamaki, kana ta bushe
da
dariyar karfin hali ganin har ya fara hada gumi
duk da na'uarar sanyaya daki da ke iya bakin
kokarinta a karamin falon.
"Zauna mana to, sarkin tsoro ina za ka?"
Ya yi ajiyar zuciya "Ai Hajiya abin ne na ji ya na
kokarin fin karfi..."
"To zauna ka fada mana!" Ta ce da daga murya.
Ya zauna a hankali.
"To mene ne ke kokarin fin karfinka?" Ta
bukata.
Ya share gumin da ya soma taruwa a goshinsa.
"Hajiya ni kin san duk wani abu in dai da yan
sanda a ciki tsoronsa na ke."
"Ka na namijin?" Ta rike baki.
"To shi namiji karfe ne bai san wuya ba?" ya ce
ya na zaro idanu. "Ai idan ki ka lura ma ko
karfe
idan ya sha wuya ya na sarrafuwa."
Hajiya Rukayya ta yakune fuska, "To ka ga
kwantar da hankalinka, in dai ina raye ba kai ba
wahala, ka na ji ko?"
Ya dube ta ya dan yi dariya "Allah Hajiya?!"
"Af, ka dauki abin wasa, kawai ka yarda ka karbi
wanan garabasar kar ka zama mai gudun rabo."
ta dan kwantar masa da hankali.
"To na ji Hajiya, wacce irin magana ce?"
Ta mike tsaye, "Ina zuwa" Ta fice daga falon, ta
bar shi zaune a nan ya na ta sake-saken zuci.
Jim kadan ta dawo, kudi rike a hannunta yan
naira hamsin-hamsin bandir guda. Ta na zuwa
daidai shi ta jefa masa a kan cinyarsa. "Ga su
nan naira dubu biyar ne, kafin ka kammala na
cika ma sauran"
numfashinsa ne ya ji kamar zai dauke da ya
dubi
kudin. Nan da nan ya dauka ya fara jujjuyasu.
Sababbi ne kal-kal. Ya nayin kallon da ya ke
musu na maita sun isa su tabbatar da a shirye
ya
ke ya aikata duk abin da aka umurce shi, tuni
ya
manta da cewa ya zo ne ya ji dalilin da ya sa
Hajiyar ta hana shi zuwa gidan shekaran jiya da
kuma kyautar dubu dayan da ta yi masa.
"Hajiya yanzu ke na ke jira.. Wacce magana ce?"
Ta yi murmushi ganin cikin dan kankanin lokaci
ta gama shawo kan Lukman da maasu gidan
rana (kudi). san kalmar a'a?" Ta bukata bayan
ta tsayar
da dubanta gare shi.
Tambayar ta ba shi dariya, "Haba Hajiya ai ko
yaron da aka yaye yanzu ya san wannan kalma.
Ita wannan kalma ai ta na amfani ne yawanci
don
nuna ba haka abu ya ke ba, na ki ko rashin sani
ga wani abu, kai har..."
"Yauwa dan gari da kai ake zance". Ta katse shi,
"To abin da na ke so ka yi kenan a duk sa'ar da
yansandan su ka riske ka don yi ma tambayoyi,
ma'ana duk abin da ka sani sai ka nuna ba ka
sani ba, abin da ba ka sani ba shi ma daman
ba
ka sani ba."
"Af, lallai aikin mai sauki ne" ya ce a ransa kana
ya bushe da dariya "Wannan ne kawai aikin
Hajiya?"
"Eh mana" Ta amsa ta na tabe baki.
"Yanzu daga wannan na ci dubu goma?"
"Kwarai kuwa." Ta tabbatar masa.
Ya kuma duban dubu biyar din da ke hannunsa,
sannan ya mike tsaye ya sa a aljihun wandonsa,
ya koma ya zauna.
"To sha kuruminki Hajiya an gama, yaushe za su
zo?"
"Kowanne lokaci daga yanzu, kai dai ka kasance
cikin shiri"
ya kuma mikewa "To ina iya zuwa gida na adana
kudin nan na dawo?"
Ta kalle shi "Ka na iya zuwa amma ka dawo da
wuri"
Har bakin kofar ta rako shi da amon muryarta
ta
na jaddada masa bukatarta, shi kuma ya na
dafe
da kudin ya na tabbatar ma ta da kada ta ji
komai.
***
Kamar yadda abin ya ke a zukatan wadanda ya
shafa, ita ma Barista Hannatu haka ya ke a
zuciyarta domin tun a jiyan da abin ya faru
bayan
ta koma gida ta kasa runtsawa, babu komai
cunkushe a zuciyarta sai mamaki da tunanin
faruwar al'amarin. Har kawo yanzu karfe bakwai
da rabi da ta shirya ta ke kokarin tafiya asibitin,
tunanin ya gaza yankewa.
To amma fa har zuwa yanzu zuciyarta ta ki ta
amince da cewa kawarta ce ta aikata laifin. Shi
ya sa yanzu ma da take tsaye gaban dogon
mudubin bayan fitowa daga wanka take
gaggawar ta tafi asibitin domin bin diddigin abin
don sanin gaskiya, a matsayinta na mai bayar
da
kariya (Lawyer)
Bayan fitowarta da nufin tafiya asibitin sai ta yi
tunanin tafiya gidan su Zainab domin sanar da
mahaifanta. Shakka babu ta san rikicewar da
kawar tata tayi zai yi wuya ta sanar da mahaifan
nata.
Sa'ar da ta isa gidan ba ta iske mahaifin Zainab
ba don tuni ya tafi kasuwa. Ko da ta sanar da
Mahaifiyar Zainab da wani yayan Zainab din da
ta samu a gidan sai su ka rikice, su ka rasa
yadda za su yi.
Daga karshe da kyar Barista Hannatu ta
rarrashe
su ta nuna musu idan Allah ya so komai zai
daidaita.
Bayan ta bar gidan kai tsaye ta wuce asibitin. Ko
da ta isa sai ta iske labarin cewa ai tun jiya
kawarta ta ke hannun hukumar binciken
laifuffuka
(Yansanda) sai ta ga ba ta ga ta zama ba. Nan
da nan ta bar asibitin ta tunkari hedikwatar
yansandan.
Ba a wannan karon ne ta taba zuwa hedikwatar
ba,
wannan shi ne karo na uku, domin a baya ta zo
kusan karo biyu don yin wasu bincike game da
wasu kesa-kesai (Cases), da ta kare, don haka
ba
bakuwa ba ce a wajen.
Kai tsaye bayan ta isa ta wuce ofishin ASP
Haladu domin saninta na cewa shi ne ofishin da
ke da alhakin wannan matsalar. Ta kuwa yi sa'a
ba ta samu cunkuson jama'a ba kamar yadda ta
sha samu a baya.
Bayan dan jira na abin da ba a rasaba aka yi ma
ta umarni da ta shiga.
A nutse cikin dankareriyar kujerarsa ta same
shi,
shi ne dai da ta sani. Shi ma bai manta ta ba.
Bayan sun ida gaisuwa, ya ce, "Barista-Barista,
yau ke ce da kanki?"
Ta yi yar dariya "Ni ce Wallahi yallabai"
"Ina ce dai kes (Case) ki ka biyo?"
Ta gyada kai kawai ba tare da ta yi magana ba.
"Yauwa ni na san dai ganin ku ba banza ba,
akwai magana" ya ce shima ya na dariya "Wane
kes ki ka biyo?"
"Yallabai na biyo kes din wata kawata ce Zainab
wadda aka kawo ta nan jiya"
Alamun dariyar da ke kan fuskarsa su ka sauya
zuwa na mamaki.
"wacce Zainab ce kawarki? Wadda ake zargin ta
aikata kisan kai? Menene hadin ki da ita?"
Barista Hannatu ta yi dan murmushin karfin hali
"Yallabai ina da ja ne game da zargin da ake
mata, domin kuwa na san zai yi wuya ta aikata,
tun da kuwa na san halayenta ciki da waje, tun
muna firamare (Primary) muke tare"
ASP Haladu ya nisa "Wato yanzu dai ki na so ki
nuna min cewar sanin da ki ka yi ma ta tun
daga
firamare zai iya hana ta aikata laifin da ake
zarginta ko? Ko mutum idan ya na karami idan
ya girma halayensa ba sa sauyawa?"
Ta girgiza kai "Ba haka nake nufi ba"
"To ya kike nufi?" A wannan karon ya na dariya
ya bukata.
"Ina nufin a yadda abin ya faru akwai dimbin
mamaki ace wadda ake zargi ce ta aikata"
"Wato yanzu dai ki na da ta cewa kenan?" ya
bukata har yanzu ya na dariya.
"Shi ne ma dalilin da ya sa na zo?"
"Ki na nufin za ki iya ba ta kariya ne?" A yanzu
ya tattara hankalinsa gare ta kamar mai kokarin
gane wani abu a tare da ita.
"Eh, kariya na ke so na ba ta da kuma bi ma ta
kadin sharrin da a ka yi ma ta na bata suna,
yanzu ina so a mika batun kotu ne?"
ASP Haladu ya fashe da dariya, kana ya ce
bayan
ya sassauta. "Na san ki na da kokari sosai wajen
tsayawa a kotu don ganin kin baiwa wanda ki
tsayawa kariya. Amma wannan karon na san ko
da ni mu ka tsaya a kotu sai na kada ke, duk da
ba aikina bane. Barista Hannatu ta dan biyewa
dariyar da ya ke
yi ciki karfin hali. "Ba ka fahimci abin da nake
nufi ba shi ya sa, saboda haka kawai ka kyale
ni.
Ina kan bakata ta ba ta kariya kuma yallabai
yanzu ina son ganinta." Ta sauya hirar.
Ya yi jim na dan lokaci sannan ya ce "Barista da
dai kin jinkirta zuwa lokacin da za mu karasa
bincike tun da yanzu mun yi nisa, domin yanzu
ma akwai wadanda na tura can gidan don su
kuma samo mana wani abu."
Ta nisa "Yanzu ba za a bar nu na ganta ba
kenan?"
Ya yi shiru ya na tunani, ya san idan ya hana ta
ganin Zainab din a matsayin wadda zata ba
kariya bai kyauta ba, dadin dadawa ba shi da
zabi don haka sai ya ce. "To yanzu ki ke son
ganin ta ko kuwa ya ya?"
Ta yi yar dariyar karfin hali (domin duk abin da
ta
ke hankalinta ya na ga tunanin Zainab din, da
halin da take ciki).
"Eh! Yallabai yanzu mana." Barista Hannatu ta
ce.
***
Idan ka kwatanta fitar Lukman da shigowar yan
sanda gidan du-du-du bai dara rabin sa'a ba.
Su
ma a zaune a falon su ka iske Hajiya Rukayyar
tare da yan zaman makokin, sa'ar da maigadi
Bukar ya yi musu jagora.
Bayan sun gaisa tare da yi ma ta gaisuwa, sai
Sifeto Habibu ya shiga yin abin da shi ne ya
kawo su, ba kama kafar yaro.
"Hajiya zan so dayan biyu cikin wadannan
abubuwan."
ya dan yi shiru sannan ya ci gaba, "Ko dai mu
kebe a wani waje ba wannan ba, ko kuma a dan
ba mu waje."
(Ya na nufin yan zaman makokin su fita daga
falon.
"A'a,mu ne dai ya kamata mu ba ku waje..."
Wata mata da ta yi matukar kama da Hajiya
Rukayya ta fada da saurin baki.
Kana ta mike ta ce da sauran matan, "Ku taso
mu koma ciki kafin su gama."
Babu wadda ta musa, sauran matan su ka mike
jiki a sanyaye su ka rufa ma ta baya, kai tsayae
su ka fice daga falon.
Sifeto Habibu ya numfasa, "Hajiya tun a jiya mu
ka so mu ji ta bakinki game da wannan
al'amari,
amma sai ya kasance ba ki ji dadi ba shi ya sa
mu ka jinkirta zuwa yau. To amma a binciken da
mu ka yi mun samu labarin cewa ke ce ki ka
sayawa yaran ita waccan alewa da ta zama silar
rayuwar yayanki... Ya ya abin ya ke?"
Ta zunkuda kafada gami da girgiza kai." Yallabai
ni ba ni na saya musu irin wannan alewar ba. Ni
alewar da na saya musu ma... Ai ba jiya ba ne
yau fa kusan mako guda kenan, kuma ace ba a
sha ba sai a jiya?"
Sifeto Habibu ya girgiza kai "Hajiya Wannan fa
an
ce a jiya ne sa'ar da ki ka kai su makaranta..."
"A'a ni jiya da na kai su makaranta ban saya
musu komai ba. Ni dana kai su a makare,
yaushe
zan tsaya na saya musu alewa?"
Ta fada ta nadaga hannu.
"Yanzu dai ke alewar da ki ka saya musu an kai
mako guda kenan?"
"Sosai kuwa, domin jiya mako guda daidai."
Ya jinjina kai "To Hajiya na ji kin ce jiya kin kai
su makaranta da kanki. Me ya sa? Ko dama ke
ce ki ke kai su? Ba ku da direba ne?"
Tambayoyin sun yi ma ta yawa don har taso ta
rikice sai da ta dau dakiku a kalla goma kafin ta
ce "Direba ne ke kai su, amma ai ranar makara
ya yi..."
"Bai zo akan lokaci ba kenan?"
Ta gyada kai "Kwarai domin har na dawo bai zo
ba.
"To bayan ya dawo ya sanar da ke dalilin
makararsa?
Ta gyada kai "Eh, bai tashi da koshin lafiya ba
ne."
Sifeto ya gyada kai a lokaci guda da nisawa.
"To bari na koma da ke baya Hajiya, a wancan
lokacin da ki ka saya musu alewar tsawon sati
da
ya shude, a ina ki ka saya musu? Itama a
hanyar
makarantar ne?"
Ta girgiza kai "A'a. Shi lokacin mun fita unguwa
ne kawai".
"To wacce iri ki ka saya musu?"
"Ah!" Ta bude baki cikin mamakin karya "Alewa
da ka sani Alewa ai Alewa ce."
"Haka ne amma ai kowacce da sunanta ko?"
"Eh, tabbas amma ni yanzu ba zan iya rike
sunan
ba domin ban kula ba."
Ya nisa da karfi "To yanzu Hajiya, ina za mu ga
matukin gidan nan, ma'ana direba."
Da ta yi niyar ta ce musu yanzu ya fita sai ta yi
tunanin kar su gano abin da su ka shirya. Sai ta
sauya da cewa Bai zo ba amma kuna nan za ku
gan shi."
Ta na rufe baki su ka ji sallama a bakin kofar
shigowa falon. "Yauwa ka ga dan halak ma, ga
shi nan". Hajiya Rukayya ta ce ta naduban
Lukman da ya daga labulen falon ya shigo.
Gabansa ya fara faduwa ganin yan sanda uku
zaune kowanne da gishin baki kamar jelar
tsuntsu, habarsu aske tas kamar bayan kasko.
"Kai sakarai kar ka nuna tsoronka tun yanzu
mana, aikin naira dubu goma fa za ka yi kuma
har an ba ka dubu biyar."
Wani sashe a zuciyarsa ya tunatar da shi.
Ya nufi daya daga cikin kujerun ya zauna.
"Sannun ku da zuwa."
"Yauwa sannu."
Sifeto Habibu ya juya ga Hajiya Rukayya. "Hajiya
don Allah dan ba mu wuri mana."
Ta yi murmushi "To". Ta mike tsaye ita ma ta
fice daga falon, sashikan zuciyarta na ta fadar
ra'ayoyinsu game da hakan.
Wasu na cewa "Shi kenan asirinki ya tonu."
yayin da wasu kuma ke cewa "Kar ki yi wata
fargaba, Lukman ba zai bayar da kafa ba.
Meyen
kudi ne fa!"
Ganin ta fice Sifeto Habibu ya tattara hankalinsa
ga Lukman. Cikin duba na kwarewa ya ce.
"Malam Lukman kai ne direban gidan nan ko?"
ya gyada kai gami da cewa "Ni ne yallabai"
"Kai kadai ne direban ko da wani?"
"A'a, ni kadai ne yallabai, ba wani". "To me ya
sa jiya ba ka zo ka kai su ba?"
Tambayar ta yi ma sa bazata hakan ne ma ya
sa
ya amsa cikin rawar baki.
"Eh, ba ni...da la...lafiya, yallabai...mura ce ke
damu...na, shi ya sa ban...ban zo ba.."
Sifeto Habibu ya jinjina kai, "Wannan shi ne
kawai ya hana ka zuwa."
"Yallabai shi ne."
"To waye ya je ya dauko su, ma'ana bayan an
tashe su?"
"Ni ne?" Ya dafa kirjinsa.
"Lokacin murar taka ta warke ne?"
"A'a, na dai samu sauki."
Sifeto Habibu ya shafi dumbujejen gashin
bakinsa
cikin kokarinsa na son sauya hirar.
"Lukman sa'ar da ka dauko yaran nan ko ka ga
wani abu a tare da su. Abin nufi a hannunsu
wanda ya danganci na sha?"
Ya girgiza kai "A'a gaskiya ban ga komai ba."
Yanzu ya dan nutsu "Sai dai ko jukukkunansu."
"Ban da wannan Lukman. Mun gode."
"Yallabai ni ne da godiya." Cewar Lukman.
Ya mike ya fice daga falon saboda umarnin
Sifeto
Habibu na sa shi ya kirawo ma sa Hajiyar.
Ba a jima ba su ka dawo tare.
Sifeto Habibu ya dube ta bayan ta zauna.
"Hajiya
yanzu za mu tafi domin mu tattara duk abin da
mu ka samu, in ya so daga yanzu zuwa daren
yau za ki ji daga gare mu. "Mun gode".
"Mu ne da godiya."Hajiya Rukayya ta ce.
Su ka mike su ka nufi kofar ficewa, har sun kai
ga kofar Sifeto Habibu ya waigo. "Ko da ya ke
Hajiya." Ya fara takowa zuwa ciki "Za mu iya
cewa yanzu mun kammala bincikenmu. Abin da
ya kamata ki sani shi ne, za mu kai ku kotu
domin warware wannan matsala a can." Ya taya
ya na duban ta sa'ar da ya kai ga tsakiyar falon
"Zan so na ba ki shawara idan ki na da lauya ki
sanar da shi domin za mu yi komai daga yau
zuwa kwana shida mu ga an kira ku."
Gabanta ne ya fara bugawa kafin ta yi fari da
kwayar idanunta, cikin karfin hali ta ce.
"To...to..yallabai..za a sanar da shi."
Sifeto Habibu ya juya ya nufi kofar inda yan
uwansa ke tsaye su na jiransa, su ka fice.
Hajiya Rukayya da Lukman su ka numfasa,
numfasawa me nauyi bayan fitar yan sandan.
"Yau na shiga uku Lukman, wai ka ji kotu za a
kai mu." Hajiya Rukayya ta fada hannunta a
dafe
da kirjinta.
Lukman da ke zaune can gefe ya zuba tagumi
ya
cira kai ya dube ta. Mamaki ya bayyana a kan
fuskarsa ganin Hajiya Rukayya ta rikice, "Hajiya
mene ne na damuwa cikin wannan al'amari? Ke
da kike da gaskiya kuma aka cuceki. Me ye cuta?
Aka kashe miki yaya har biyu. Haba! Wannan ai
kamata ya yi ki fi kowa farin ciki kuma..."
"Ba haka bane Lukman ka san fa kotu da bin
diddigi."
"Ammaai daga karshe gaskiya ce take nasara
ko?"
Das! Sai da gabanta ya fadi kafin ta ce.
"Eh, ha...ka ne, amma ni da an yafe.."
"Waye zai yafe Hajiya ai ko ke kin yafe yan
sandan nan ba za su yafe ba. Saboda haka
kawai
ki saki jikinki a karbo miki hakkinki."
Ta nisa kana ta sa hannu ta share gumin da ya
soma jika ma ta goshi. A lokaci guda kuma sai ta
fara tunanin zuwan Baraka kawarta sa'ar da ta
isketa a daki zaune har kawo sa'ar da su ka
dawo daga gidan boka. Ta na tafe har lokacin
da
Mujahid ya iske ta a dakin girki ya sanar da ita
farkon faruwar mummunan ala'amarin, kawo
lokacin da likita ya ce sun mutu zuwa yanzu da
yan sandan su ka gama bincike su ka ce wai za
su mika kotu daga nan zuwa kwana shida. Nan
da nan zuciyarta ta shiga hadawa da tantance
riba da rashinta a cikin al'amarin. Cikin kankanin
lokaci sai ta gano cewa babu wata riba da aka
samu ko alama, domin kuwa na farko Wanda fa
su ka yi domin shi (Dan kishiyarta Mujahid) na
nan da ransa yanzu haka. Na biyu yayan ta biyu
duka sun mutu, su na da gado kuwa? Tun da an
ce shi Alhaji Basiru da sauran numfashinsa. Abu
na uku wanda kuma shi ne uwa uba wai za aje
kotu, gurin da ta tabbatar idan ta shiga asirinta
ya gama tonuwa, daga ya tonu kuma ba ita ba
sauran rayuwa domin ta san zai yi wuya ta tsira.
Nan da nan sai ta ji zuciyarta ta shiga kogin
nadama da dana-sani, a fage daya kuma da
zargi
gami da la'antar matar da ta sa ta a wannan
tafarki, Baraka.
Ta kuma nisawa da karfi a karo na biyu, take sai
ta ji kwalla ta soma kwararowa daga idanunta.
Lukman da bai san me take tunani ba sai ya ji
ya
kagauta ta gama abin da ta ke yi shi ta cika
masa sauran kudinsa ya yi tafiyarsa domin ya yi
alkawari a zuciyarsa gari na wayewa zai yiwa
kasuwar kantin kwari tsinke domin samo yan
atamfofin da zai ganganda ya aika gidan yar
bazawararsa Bintoto, shi fa aure ya ke so. Shi
ya
sa ya kasa bata dama ta ci gaba da tunanin ya
ce.
"Hajiya, ni ina ga kawai ki yi hakuri ki dake kotu
za ta kwatar miki hakki. Yanzu abu guda da
nake
ganin ya dace ki yi kawai ki nemi lauya.."
sai yanzu ta ji magana domin ko babu komai dai
bata da wani zabi da ya wuce ta binciko lauya
da
zai tsaya ma ta, don haka da Lukman ya tabo
wannan bangaren sai ta cira kai ta dube shi.
Murya a shake ta ce "Lukman a ina kake ganin
zan samu lauyan... Ka san fa ni ban san yadda
zan yi ba."
Ya ji dadi ya ji ta bude baki ta yi magana domin
ya san in dai za ta ci gaba da magana da shi to
sauran kudin sa ma za su fito.
Ya sosa kansa "Hajiya ai wannan mai sauki ne,
ko anan unguwarmu ma akwai wani da na
sani..shi ma lauya ne." Ta ji dadin hakan da ya
fada. Ta sa gefen
gyalenta ta goge hawayen dake zuba daga
idanunta.
"Lukman! Kana nufin anan unguwar ku akwai
lauya?"
Ya gyda kai "Kwarai kuwa Hajiya makwabcinmu
ne ma."
"To yanzu ya za a yi mu gana?"
Ya sunkuyar da kansa cikin yunkurinsa na son
tuno lokacin da ya san Barista Garba Shehu ke
zama a gida.
Ya cira kai ya dube ya bayan ya tuno, "Hajiya na
kan yawan ganinsa a gida da yamma...kai, ko
yau ma idan aka yi sa'a za a iya samunsa bayan
La'asar."
Ta numfasa cikin gamsuwa "To yanzu nan zan ce
ya zo ko ni ya kamata na neme..."
"A'a Hajiya ai zai fi kyautatuwa ki neme shi." Ya
katse ta. "Shi wanda ka ke nema a wajensa ai
samunsa ya dace ka je ka yi."
"Haka ne!" Ta ambata ta na gyada kai, "To
yanzu
yau din ya dace mu je mu gan shi ko?"
"Kwarai kuwa ai da safiya ake kama fara."
"To shi kenan". Ta mike tsaye "Idan anyi sallar
la'asar ka zo ka kai ni wajensa, kuma ina zuwa".
Ta nufi wata ko far dake manne cikin tafkeken
falon.
Ya so ya ce ma ta dubu biyar dinsa, amma
ganin
tana sauri kuma ta ce masa ta na zuwa sai ya
kyaleta.
Ba ta jima ba ta fito ta iso daidai kansa ta mika
masa.
"Ga cikon kudin ka Lukman. Dan Allah kar ka
bata lokaci hudun na yi ka zo mu je."
"An gama Hajiya." Ya ambata sa'ar da ya damki
kudin, tamkar mai kamun fara. "Da zarar lokaci
ya yi za ki ganni". Ya mike "Ko yanzu ma idan
na
koma gida da zarar kin gan ni na dawo to fa ya
na nan sai kawai ki shirya mu je."
"Yauwa Lukman don Allah ka kokarta". "To"
Har ya je bakin kofa da kudin a hannu sai ya
tuna
take ya tsaya kamar an kira sunansa daga baya,
ya cusa kudin a aljihunsa ya yin da zuciyarsa ke
cewa.
"Lallai komai taurin ruwa in an jefa dutse sai ya
lume a ciki. Ka duba tsumulmula irin ta Hajiya
amma da yake Allah ya kwata min. Gashi zan yi
arziki ta dalilinta..."
Da haka ya fice daga falon."
***
SABANIN dazu da ta bar ofishin ASP ba kowa ta
je ta ga kawarta, yanzu ofishin akwai mutane a
ciki.
Wannan ne ya sa ta samu waje ta zauna a falon
ofishin ta najiran su fito ta shiga, zaman da ya
ci
gaba da tariyo ma ta faruwar dagulallan
al'amarin garai-garai kamar a allon sinima.
Shakka babu kallo daya za ka yi ma ta tabbatar
cewa ta na cikin halin matsananciyar damuwar
da
ke bukatar tallafin gaggawa, jifa-jifa abin da
kawarta ta ke yawan ambata ne yayin da ta je
wajen ta yanzu, ke fadowa cikin zuciyarta.
-Wallahi summa tallahi Hannatu ban san komai
game da wannan alewa ba har sa'ar dana
dauko
ta na kawo...ba ni na samar da alewar
ba...wallahi ba ni na samar da ita ba." Kuka ne
ke biyo baya, kukan da ke sa zuciya kuka.
Ta numfasa kamar dai yadda ta ke yi duk
lokacin
da ta tuno wannan kalami mai karya zuciya,
wanda a wani sashen zuciyarta kuma shi ne ke
sawa ta kara jin kwarin guiwa akan kudirinta na
kare ta da kwato ta daga wannan kangi.
To a daidai lokacin da ta numfasan ne mutanen
da ke cikin ofishin (wanda su take jira su fito ta
shiga ciki) su ka fito.
Da gaggawa ta mike ta cusa kai cikin ofishin.
"A'a...! Barista har kin dawo?" Tun kafin ta
gama
mayar da kofa ASP ya ce hakan, ya na duban ta
cikin bayyanar da wani malalacin murmushi.
Ita ma ta mayar masa da murmushin bayan ta
rufe kofar, sai dai babu bambanci da irin wanda
ya yi mata, "Eh, yallabai na dawo" Ta ce a
sanyaye.
"Sannu da zuwa...Bismillah.." Ya ba ta umarnin
zama.
"Yallabai na je na gan ta." Ta ce bayan ta zauna.
"To amma ina neman wata alfarma."
Ya tsayar da idanunsa ga kallon ta bayan ya dan
tsuke fuskarsa. "Wace alfarma kuma ki ke nema
bayan wadda ki ka nema ta, a kai ku kotu?"
Ta nisa, "Ban da wannan yallabai don ita dama
ba alfarma ba ce, tunda kuwa wajibi ne ku kai
kotu ko da ban nema ba, sabo..."
"To na ji yanzu wace alfarmar ki ke nema?" Ya
katse ta, a kagauce gami da tambaya don kuwa
ya san gaskiya ne abin da ta fada ko ba ta
nema
ba tilas a kai maganar kotu.
Ta dan yi murmushi, "Haba yallabai mene ne na
harzuka, sai ka ce wadda na ce ka sake ta?"
Ya mayar da bayansa ga majinginar kujerar ya
jingina,
"To ai ke ce na ji ki na so ki yi min tsari kamar
wadda aka hau kotu".
"O.k, dama su lauyoyi tsari suke yi?" Ta ce
bayan
ta kada kai gefe.
"Kin ga ni ban ce ba." ya daga hannu, "Kar ki
kai
ni gaba."
Su ka yi dariya tare.
"Don Allah wace bukata ce, fadi, don ina da aiki
mai yawan gaske a gabana, kin ga bayan fitarki
ma an kawo min rahoton wani bincike da aka yi
dazu a can gidan, ina so a hada shi a shigar
kotu. Idan so samu ne a ce Litinin kun hallara a
kotun."
Ta sunkuyar da kai, jim kadan ta dago ta dube
shi,
"Yallabai akwai halin a bayar da belinta kafin
zuwa kotun?"
Ya girgiza kai, "No! No!! No!! This is non bailable
offence Hannatu (a!a!!a!!! Wannan ba laifin da
ake
ba da beli ba ne Hannatu) Abu guda kawai da
zai
sa a sake ta shi ne, a yi shari'a a tabbatar ba ta
da laifi. Idan ta wanku daga abin da ake zargin
ta, to sai kotu ta sake ta".
Barista Hannatu ta kuma dukar da kai. Ba ta da
ta cewa, domin ta san hukuncin kenan. Daga
karshe haka ta hakura ta baro hedkwatar
yan sandan da zummar zuwa ta fara bincike
akan
dan abin da ta tattara da wanda ta samu a
bakin
Mujahid kafin ranar Litinin, duk da cewa ta yi-ta
yi ya bi ta ya ki yarda.
***
Karfe hudu da kwata na yamma Lukman direba
ya daidaita tsayuwar motar kirar "KIA" a kofar
gidan lauya mai zaman kansa Barista Garba
shehu, kwararre, gogagge kuma fitaccen lauyan
da lauyoyi ke shayin karawa dashi.
Cikin sauri ya fito bayan ya kashe motar, ya
budewa Hajiya Rukayya kofa.
Sannu a hankali kamar mai cikin wata tara ta
fito. Ya mayar da murfin a hankali ya rufe.
"Hajiya, nan ne gidan!" Ya yi ma ta nuni da dan
madidaicin gidan mai dauke da farin fenti, da
su
ke tsaye gabansa.
Gidan ba ya cikin sahun gidajen kece raini idan
har za a tsunduma shi cikin jerin gidajen ma su
hannu da shuni.
To amma duk da haka shi ma ba laifi don ko ba
komai dai shafe ya ke da sabon fentin farar
kasa.
"To yanzu ya za a yi mu tabbatar ya na ciki?"
Hajiya Rukayya ce ta bukata.
Lukman ya yi yan waige-waigenshi, "Kin ga wani
lokaci fa, a nan kofar gida ma za ki gan shi,
amma..."
Wani yaro ya hango shi ya sa maganar tasa ta
katse.
"Kai! Zo mana!" Ya ce da yaron bayan ya yafito
shi da hannu.
Bai yi gardama ba ya tunkaro su.
"Hajiya bari mu tura yaron nan ya kira shi." Ya
ce
bayan yaron ya iso gare su.
Ba ta yi magana ba, gyada kai kawai ta yi.
"Kai don Allah shiga nan gidan kace ana sallama
da barista.."
"Nan gidan?" yaron ya bukata ya na mai nuna
gidan da yatsansa.
"Eh, nan".
Bai sake magana ba ya nufi gidan ya shiga, jim
kadan ya fito. "Wai an ce ya na zuwa." Tun kafin
ya iso wajen su ya fada.
"Yauwa yaro, mun gode ka ji?" Lukman ya ce
kana ya dubi Hajiya Rukayya, "Hajiya mu
tsallaka
daga kan dakalin ko?"
Suka tsallaka. Daidai lokacin ne Barista Garba
Shehu ya fito.
Fari ne, ya na da yar kiba amma ba can ba,
haka
zalika shi ba dogo ba kuma shi ba gajere ba. Ya
na da yawan fara'a daidai gwargwado.
"A'a, Lukman kai ne kake sallama." Abin da ya
fara fita daga bakinsa kenan.
"Barista Garba Shehu!" Lukman ya ce gami da
daga hannu cikin jinjina.
Barista ya mika masa hannu su ka gaisa, kana
ya
duba Hajiya Rukayya da ke faman kallonsa tun
sa'ar da ya fito, ya ce, Hajiya ina wuni?"
Ta dan saki fuskarta kadan "Lafiya lau, ya gari,
ya aiki?"
"Lafiya Sumul Hajiya" ya amsa.
"To madalla, sannu!"
"yauwa sannu."
Lukman ya dubi Barista bayan sun ida gaisuwar,
"Barista wajen ka mu ka zo takanas ta kano."
"Ni ko?" ya yi murmushi.
"Kwarai kuwa." Ya gyada kai.
"To ai ina ga zai fi kyautatuwa mu shiga daga
ciki
ko?"
"Duk yadda ka ce." A wannan karon Hajiya
Rukayya ce ta fada ta na murmushi.
"Ina ga zai fi kyau...ku zo mu shiga daga ciki."
Barista ya ce, sannan ya juya su ka dafa masa
baya kamar jelar dawisu har cikin madaidaicin
dakinsa.
Dakin ba laifi kwarai da gaske. Daga kasa ya na
shimfide da wani shudin kafet mai taushin
gaske,
ga wata tattausar katifa wadda a ka sa daga
kusurwar yamma maso arewacin falon. Daga
gabas maso kudancin falon kuwa wani dan
teburi
ne da ke daure da akwatin talabijin mai launi
da
bidiyo da kuma katuwar radiyo, rikoda. Daga
samansu kadan an fasa bangon an zuro na'urar
sanyaya ko dumama daki (Air Condition) duk
ilahirin jikin bango kuwa zagaye ya ke da labule,
hakan zai iya hana gane launin fentin da bangon
ke dauke da shi. Sakale a sama wata
kyakkyawar
fanka ce ke ta faman aiki abin ta ba
kakkautawa.
Bayan sun zazzauna su ka kuma gaisawa.
"Barista wasu yan matsaloli ne ke tafe damu."
Lukman ya soma, "Shi ya sa ka ji na ce ma
wajenka mu ka zo takanas."
Barista ya gyada kai cikin saurare.
"Ko da ya ke..." Lukman ya ci gaba bayan ya
juya ga Hajiya Rukayya, "...wannan ita ce Hajiya
Rukayya matar maigidana Alhaji Basiru, kuma
ita
ce ta kasance cikin wannan matsala. To da aka
ce ana neman lauya, shi ne na shaida ma ta
cewa akwai ka, saboda haka na yi ma ta jagora
zuwa gare ka."
Barista ya gyada kai cikin gamsuwa, "Wannan
gaskiya ne. Hajiya wace irin matsala ce
wannan?"
Hajiya ta dube shi, cikin maraireta ta kwashe
labarin abin da ya faru kaf na karya ta sheda
masa.
Barista ya jinjina kai bayan ta kawo karshe.
Lallai
ko shakka babu da alama shi ma abin ya ba shi
mamaki.
Domin sai da ya jima kansa a duke kana ya
dago
a hankali, "Hajiya sannu kin ji, Allah ya ji kansu
ya kuma gafarta mu su."
"Amin...!" Lukman ya amsa.
Hajiya Rukayya kuwa tuni ta soma kuka.
"Ki yi hakuri Hajiya, ki kwantar da hankalinki da
yardar Allah zan tsaya tsayin daka akan wannan
al'amari don ganin kin samu hakkinki." Ya dan
tsahirta kana ya ci gaba, "Yanzu ina kanin mijin
naki, da abokinsa?"
Ta sa mayafi ta tsane hawayen dake zuba daga
idanunta, cikin muryar kuka ta ce, "Suna can,
asibi...ti, su na kula da Alhajin.
"Wanne asibitin kenan?" Ya kuma bukata.
"Asibitin lafiya jari."
"Ok, a nan suke?"
"Umn." ta gyada kai.
"Shi kuma likitan da ya zo lokacin faruwara abin
fa?"
"Shi ma..acan ya ke".
"Wato ita dai yanzu amaryar ta ki ta na tsare
ko?"
"Eh!" Ta amsa. "To mu na godiya Barista."
Lukman ya ce sa'ar
da su ka mike da zummar tafiya.
Har bakin motar su ya raka su, su ka tashe ta
su
ka tafi. Hajiya na farin ciki ganin zata samu
kariya a wani bangaren kuma ta na mamakin
kankanta da karancin shekarun na lauyan da zai
tsaya mata.
***
A kokarin ta na ganin ta kubutar da kawarta
daga
cikin matsalar. Washe gari bayan ta gama
kintsawa ta yi karin kumallo, ta fita ta nufi gidan
Alhaji Basiru da zummar son ganawa da
Lukman,
a matsayin mutum na farko da ta ke son ta fara
bincika.
Lokacin da ta isa gidan, ta yi matukar sa'a da ta
same shi zaune cikin harabar gidan, shi da
maigadi Bukar.
A gajarce su ka gaisa, kana Barista Hannatu ta
bukata, "Don Allah ko Hajiya na ciki kuwa?"
"A'a! Ba ta nan." Lukman ne ya amsa mata, "Ai
ta na asibiti, tun dazu na kai ta."
Hannatu ta gyada kai, "Ko kai ne Lukman?" Ta
bukata ta na duban sa.
"Eh, ba shakka ni ne." Ya tabbatar ya na jinjina
kai.
Ta yi ajiyar zuciya, "Ka ga kuwa ina son ganin
ka."
"Ni ko?" Ya dafa kirji.
"Kwarai kuwa." Ta amsa masa.
"Na taso kenan?"
"Zan so hakan". Ta ce a takaice.
Ya dubi Maigadi Bukar da ke taunar goro
abinsa,
"Malam Bukar ina zuwa" ya mike su ka dan
kebe
can gefe gindin wata kyakkyawar shukar fulawa
mai yado.
Ka sa jurewa ya yi bayan sun tsaya, kafin ta yi
magana, yace, "Hajiya, na ce dai ko lafiya?"
Ta tsaida kallon ta gare shi ta na murmushi,
"Lukman ka gane ni ko?"
"Sosai ma kuwa. Ba ke ce Hannatu Kawar
amarya ba?"
"Lallai kuwa, ko ka san abin da ya kawo ni?"
"A'a, ina zan sani ba ki fada ba, ni da ba Allah-
musuru ba?" Ya ce da wata irin tattausar murya.
"Kana da gaskiya, na zo ne na yi ma ka wasu
yan tambayoyi, a matsayinna na lauyar da za ta
ba amaryar maigidanku kariya. Ka san za a kai
su kotu ko?"
Ya hadiyi yawu da kyar, "E...na..sani." Ya amsa
cikin in-ina. Wannan ya biyo bayan kin jinin
tambaya da ya yi a daidai wannan dan rukunin
saboda ya san komai na iya faruwa tun da shi
ma mai laifi ne. Kai! Idan ma ban da ya na
tunanin idan aka je kotu Hajiya Rukayya ta yi
nasara zai iya samun wani alkhairi daga gare ta,
ai da tuni ya tsere kauyensy, (Gamadidi).
Kafin ta kuma magana ya ce, "Me ki ke so ki
tambaye ni?"
Ta yi kasa-kasa da muryarta, "Dalilin rashin
zuwanka kai yara makaranta shekaran jiya, na
ke
so na ji."
Ya yi atishawa "Ai na jima ina amsa wannan
tambayar. Ba ni da lafiya ne."
"To ya a ka yi da rana kuma lokacin tashi ka je
ka dauko su. Ka samu sauki ne?"
"Na ji dama-dama lokacin." ya amsa da gyada
kai.
"Idan ka tashi daga aiki, abin nufi bayan ka
dauko yara daga makaranta, kana tafiya da
mota
gida ne?"
"A'a ya girgiza kai, "Ba na tafiya da ita duk a
nan
su ke kwana."
"To a wannan rana ya aka yi ka tafi da mota
gida. Ko ka san da ma za ka tashi da rashin
lafiya? Kuma da rana za ka warke, shi ya sa ka
tanade ta don kawai ka wuce daga can?"
Tambayar ta kwarzanar masa zuciya don take
launin fuskarsa ya sauya. Shiru ya yi cikin gaza
amsawa.
"Ya na ji ka yi shiru, ko ba amsa?"
ya girgiza kai "Ba haka bane..."
"To ya ya ne?"
"Shi ne abin da nake so na tuno."
Ta yi murmushi. "Ko na ba ka lokaci ka tuna?"
"Da dai zai fi." Ba haka ya so ya ce ba, dole ce
kawai ta sa shi fadar hakan da gudun tonawa
Hajiya Rukayya asiri.
Ta kuma yin murmushi, "To bari na baka dogon
lokaci don ka tuna. Ni zan tafi." Ta motsa
sahunta, ta yi taku biyu.
Ya dube ta, "Sai yaushe kenan?"
"Sai mun kuma haduwa." Ta bar shi nan tsaye
ta
nufi maigadi Bukar da tuni ya soma sana'ar tasa
gyangyadi.
"To Baba ni zan koma." Ta ce a tausashe.
Ya cira kai firgit ya dube ta, "Uhum, yar Baba a
sauka lafiya." Da a lokacin za a tambaye shi da
wa ya yi magana, ba zai iya fada ba saboda
gyangyadi da ya ci karfinsa.
Bayan barinta gidan ba ta zame ko ina ba sai
asibiti.
Likita Idris shi ne na biyu cikin jerin mutanen da
ta ke son ganawa da su, koda ya ke shi ba
kamar
sauran ba, wani taimako ta ke bukata daga gare
shi.
Ta taki sa'a kuwa, shi kadai ta iske a ofishin
nasa ya na ta faman aikace-aikace.
"Likita ya mai jikin?" Abin da ta fara fada kenan
bayan sun gaisa.
"Jiki da sauki Hannatu, ai koda yaushe ya na
samun rangwame."
"To, Allah ya kara sauki"
"Ameen-ameen."
Shiru ne ya dan gifta tsakaninsu.
"Likita na zo ne don neman wani taimako gare
ka, koda ya ke ya na da matukar fa'ida na
sanar
da kai matsayina cikin wannan al'amari bayan
na
amintaka ta da Zainab." Ta bude jakarta ta
dauko
wani kati na shaidar aiki (I.D Card) ta mika ma
sa.
Bai yi magana ba ya karba. Ya yi nazarinsa a
hankali tun daga gaba har zuwa baya. Yanzu ya
gane matsayin nata.
Ya nisa, "Ga shi Hannatu." Ya mika ma ta.
Ta sa hannu ta karba kana ta ci gaba da cewa,
"Likita ina so na ba Zainab kariya a game da
wannan badakala, shi ya sa na soma bibiyar
al'amarin."
"Wannan haka ya ke." Likita Idris ya ce ya na
gyada kai, "To na ji kin ce ki na neman taimako,
na mene ne?"
Ta kura masa idanu, "Likita, idan dai har da
yiwuwar hakan ina so ka ba ni sakamakon da ka
samu na wannan guba a rubuce." Bai yi
tsammanin shi ne taimakon da za ta nema
ba. Ya yi murmushi, "Barista wannan ai mai
sauki
ne, bari na ga?" Ya jawo dan abin adana
takardu
da ke makale jikin teburinsa, ya dauko wani
fayal
kana ya mayar ya rufe, kai tsaye ya bude fayal
din ya fara bincike. A hankali ya zaro wata
takarda a ciki, ya yi dan nazarinta.
"Barista wannan shi ne sakamakon." Ya mika
ma
ta.
Ta sa hannu ta karba ita ma ta yi nazarinta. Ta
cira kai ta dube shi, "Likita ya za a yi na samu
kwafin wannan takarda?"
"Kamar yaushe ki ke so?"
"Ko yanzu ma."
Ya nisa, "To za ki iya jira na na rubuta miki
wata?"
"Me zai hana?"
Ya mika hannu ya karbi takardar, kana ya dauko
wata takardar cikin gaggawa ya soma rubutawa.
Bai dau lokaci mai tsawo ba ya kammala, ya
mika ma ta.
Ta karba, "Na gode likita." Bayan ta dan
dudduba
ta mike tsaye, "Ni zan tafi."
Shi ma ya mike, "To barista, godiya na ke."
"Ni ce da godiya." Ta ce ta na murmushi. Har ta
kai ga bakin kofar ficewa daga ofishin sai ta
juyo,
ta dubi Likita Idris wanda tuni ya zauna, "Likita
Alhaji Sambo da Alhaji Gali fa, ko su ke jinyar
Alhajin?"
Ya gyada kai, "Su ne, kuma su na nan don dazu
na shiga wajen na gan su."
Ta kama hannun kofar ta murda, "A daki na
nawa
su ke?"
"Daki mai lamba na ashirin da daya."
Ta gyada kai, "Na gode." kana ta bude kofar ta
fice, ta nufi dakin da likitan ya sanar da ita da
zummar ganawa da Alhazan biyu, mutane na
uku
cikin rukunan mutanen da ra ke son ganawa da
su.
Lokacin da ta isa ga dakin ta tura kofar ta shiga,
su na zaune su uku, Alhaji Gali, Alhaji Sambo da
Hajiya Rukayya, a kan kujera. Shi kuma Alhaji
Basiru kwance ya na barci, robar karin ruwa
makale a hannunsa.
Salla ta yi mu su.
Da kyar su ka amsa kamar an yi musu dole
musamman ma Hajiya Rukayya da ke kallon
Hannatun a wulakance.
Ba ta damu da abin da su ka yi mata ba ko
kadan, maimakon hakan ma sai ta ce,
"Sannunku
Hajiya! Ya me jikin?"
"Jiki da sauki". Alhazan biyu ne su ka amsa, don
ita Hajiya Rukayya ma dauke kanta ta yi gefe
guda.
Ta isa ga wata kujera daidai lokacin da take
cewa, "Allah ya kara sauki."
"Ameen." Su ka kuma amsawa.
Ta zauna a hankali ita ma ta yi shiru kamar
yadda su ka yi, tsawon dakiku talatin su na a
haka.
Can ta nisa ta dubi Alhazan "To! Ni zan koma,
Allah ya ba shi lafiya."
"Ameen". Su ka amsa.
Ta mike a hankali ta kuma mayar da dubanta
gare su,
"Alhaji don Allah ina da bukatar tattaunawa da
ku."
kafin su yi magana. Hajiya Rukayya ta kalle ta
da
sauri, "Kamar ya ya ki na son ganin su su na
zaman jinya? Idan wata magana ce ki yi anan
mana."
Ta yi murmushi, "Hajiya ba wani lokaci za a
dauka ba.
Ga ni na yi bai kamata mu yi a nan ba saboda
mara lafiyar."
Ta daka ma ta harara, "To ba za su..."
"Ya isa Hajiya." Alhaji Gali ya dakatar da ita,
"Bari mu je." ya taba Alhaji Sambo, "Tashi mu
je."
Su ka mike.
Hannatu ta dubi Hajiya Rukayya, "To Hajiya sai
an jima, Allah ya sauwake".
Ta muguda baki, "Amin idan da gaske ki ke."
Barista Hannatu ta juya su ka bi ta a baya zuwa
waje.
Wani dan benci su ka samu bayan sun fito
farfajiyar asibitin.
"Bismillah ga wajen zama!" Ta nuna musu dogon
bencin. Bayan sun zazzauna, ta gabatar mu su
da kanta a matsayin lauyar da za ta ba kawarta
Zainab Kariya.
Sun yi mamaki...ba su yi mamaki ba. Mamakin
da su ka yi shi ne, ya za a yi Hannatu ta ba
matar da a ka tabbatar da ita ta bayar da
wannan guba kariya..ta wace hanya? Rashin
mamakin kuwa shi ne. Dole ne ta yi hakan
musamman da su ka duba cewa kawarta ce.
"Ina so na yi muku wadansu Yan tambayoyi ne."
Ta ci gaba bayan sun fahimci ko ita wace ce.
"A game da me fa?" Alhaji Sambo ne ya bukata.
"A game da abin da ya faru shekaran jiya,
kasancewar ku na cikin falon abin ya faru."
"To mece ce tambayarki?" Ya kuma cewa, a
hasale ya ke maganar.
Ta shafi goshinta "Alhaji a matsayinku na
wadanda mu ka bari a falon, bayan fitar mu, ya
a
ka yi su Alhaji su ka kasance cikin halin da mu
ka dawo mu ka riske su?"
Alhaji Gali ya dube ta, "Su yaran kawai gani mu
ka yi sun fadi, kuma Alhaji da farko cewa ya yi
cikinsa ya na ciwo, kamar wasa shi ma sai ya
fado daga kan kujera, duk kuma a kusan lokaci
guda."
"Daga nan kuma sai a ka yi ya ya?" Ta ce ta na
kallon su ido cikin ido.
"Daga nan sai mu ka jiyo Ihun Hajiya Rukayya,
sannan kuma sai mu ka ga sun shigo falon."
Barista Hannatu ta shafi kuncinta, "Don Allah ko
za ku iya tuna abin da Hajiya Rukayyar ke
ambata cikin ihun nata?"
Shiru su ka yi na dan lokaci kana Alhaji Sambo
ya ce,
"Kwarai na tuna."
"Me ta ke cewa?"
"Cewa ta ke kar ku sha alewar nan, alewar ba
ta
da kyau."
"Me ya sa ta ce hakan, daman ta san ba ta da
kyau ne, ko kuwa?"
Shiru su ka kuma yi su ma su na tunanin abin a
zuciyarsu.
"Haka ne fa! Ya aka yi ta san alewar ba ta da
kyau."
Zuciyar Alhaji Sambo ce ke juyayin abin. Lallai
akwai alamar tambaya anan.
Ganin sun yi shiru babu amsa, sai Hannatu ta
ce,
"To idan wannan ma ba komai ba ne, ko za ku
iya tuna abin da Hajiyar ke fada cikin surutunta
na jiya yayin da mu ke zaune muna jiran fitowar
likita?"
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
Bakin Kishi 4
Posted by ANaM Dorayi on 11:16 AM, 29-May-15
su na da yawa Hannatu wanne daga ciki?"
"Ba ku ji ta naambatar Baraka cikin sambatunta
ba?"
"Lallai mun ji." su ka amsa a tare bayan sun
tuna.
"To wace ce Baraka da har Hajiya Rukayya ke
cewa, Baraka ya haka?"
Basu da amsa kuma shi ma lallai sun tabbatar
abin tambaya ne.
"Ba mu san ta ba Hannatu." Alhaji Sambo ya ce a
sanyaye, yanzu kusan duk jikinsu ya yi sanyi
kuma hakika su na son wadannan amsoshin, to
sai dai duk wannan kafin su hada ido da Hajiya
Rukayya ne, tuni za su manta.
Barista Hannatu ta nisa, "To shi kenan na yi
matukar godiya da wannan lokaci da ku ka ba ni,
ni zan koma."
Ta mike, su ma su ka yi godiya su ka koma ciki
cike da raba daya biyu a zukatansu.
Bayan ta bar asibitin, ba ta zame ko ina ba sai
ofishinta na musamman da ke kan titin Gwarzo
domin tattara abubuwan da ta samu, da ya ke
sha biyun rana ta yi, idan ya so daga bisani idan
yamma ta yi sai ta tafi ga mutun na karshe a
cikin bincikenta, wanda ke sayar da kayan lashe-
lashe a makarantar su Mujahid.
Bayan an yi sallar La'asar ta bar ofishin ta nufi
makarantar, sai dai ta yi matukar takaici da aka
shaida ma ta saurayin Habu mai kanti ya yi
tafiya, kuma ba zai dawo ba sai gobe. Haka ta
hakura ta baro makarantar ba tare da ta sami
komai ba.
ZAMAN KOTU NA FARKO
Arewa majistiri, Babbar kotu ce da ke da fadi da
tsayin gaske. A bisa kiyasi kotun ta na daukar a
kalla mutane dari da hamsin. Amma a yau take
ta
ke da yan kallo, haraba da wajen ta, babu
masaka tsinke.
Misalin karfe tara daidai babbar bakar motar
yansandan (Irin wadda ake daukar yan fashi) ta
shiga farfajiyar farko da aka tanada don ajiye
motoci. Tsayawarta ke da wuya wasu dandazon
jama'ar da su ka makara da shiga kotun su ka
zubawa motar idanu.
Bayan kashe ta, yan sandan dake ciki su ka fito
da Zainab da ke daure da ankwa a hannu daga
bayan motar, kai tsaye su ka shige da ita cikin
kotun, da kyar da turereniya, saboda tasowa da
jama'ar su ka yi cikin hargowa, wasu na la'antar
ta da tsinuwa, wasu kuma na zagin ta gami da
Allah wadai.
Su kuwa lauyoyi tuni sun hallara a sababben
dakinsu tun kafin isowar yan sandan.
Rabin sa'a da zuwan yansandan mai shari'a
Mukhtar kano ya iso, kai tsaye shima ya shige
cikin dakin da aka kebe masa kafin shigowa dakin
shari'a.
Jim kadan lauyoyin su ka shigo cikin kotun, su ka
zazzauna a kebabben wajensu.
Barista Hannatu, lauyar da ta shigo dakin shari'ar
yau don kare kawarta, fara ce kyakkyawar gaske,
ta na sanye da irin bakaken kayansu da su ka yi
matukar yi mata kyau. Ta na rike da takarda,
farin gilashi dane a fuskarta. Sai dai kuma babu
fara'a a tare da fuskar tata, meyiwa saboda ta
san ita ce ke da karancin magoya baya a cikin
kotun, musamman da ta yi la'akari da yadda aka
rika sanar da shari'ar a kafafen yada labarai na
cewa, ana zargin kawarta da laifin kashe yayan
kishiyarta har da yunkurin kashe mijinta.
Mintuna biyar su ka rage karfe goma ta cika, mai
shari'ar ya shigo cikin dakin shari'ar. Wannan ya
sa jama'ar dake dakin gaba daya su ka mike
cikin mutuntawa. Mai shari'a ya dan rankwafa
cikin girmamawa ga jama'ar, su ma su ka
rankwafa cikin karamci kana ya zauna, su ma su
ka zauna.
A yanzu dakin shari'ar tsit ya ke kamar babu
kowa, don son jama'a na jin me zai biyo baya.
Koda aka tabbatar kowa ya nutsu, sai me karnto
shari'ar Furoskito Nura Salihu ya gabatar da
shari'ar da za a yi kamar haka:
"A yau litinin ashirin ga watan goma sha biyu
shekara ta dubu biyu da uku (20/12/2003) za mu
saurari shari'ar Hajiya Zainab Iliyasu Umar a kan
zargin da ake yi ma ta na kisan yayan kishiyarta
guda biyu, wato Hajiya Rukayya da kuma yunkuri
ko saka mijinta a halin kaka-ni-kayi, wanda har
zuwa yanzu ya na kwance rai a hannun Allah."
Bayan kammalawarsa sai hayaniya ta kunno kai
tsakanin jama'ar kowa na fadr albarkacin bakinsa
cikin tsana da kyamar Zainab.
Idan ka dauke mahaifin Zainab, Malam Iliyasu
Umar da Iyalansa, babu wanda ba ya surutu a
dakin shari'ar.
"Kamar yadda mai gabatarwa ya gabatar." Mai
shari'a ya soma, bayan ya tsawatar an yi shiru,
"Yanzu ba tare da bata lokaci ba, za mu saurari
karar daga bakin jami'in tsaron da ya shigo da
ita, wato Sufeto Habibu."
Wani dogon Dan sanda ke zaune a gaba-gaba ya
mike, hannunsa rike da wasu takardu, ya nufi
mumbarin da masu amsa tambaya ke hawa, ya
hau. Bayan an rantsar da shi, ya soma gabatar
da karar cikin daga murya.
"Godiya ta tabbata ga Allah madaukakin sarki, da
ya ba mu dama da ikon kammala wannan
bincike, akan wannan mummunan laifi na aikata
kisan kai, ta sigar yaudara, wanda Zainab Iliyas
ta yi ga yayan kishiyarta Hajiya Rukayya.
"Ya mai shari'a wannan al'amari ya faru ne a
yammacin ranar lahadi sha biyu ga watan biyu na
wannan shekarar.
"Kamar yadda sakamakon bincike ya nuna akan
wadda ake zargin (Zainab) ta samar da wata
Alewa ne mai guba, da ita ce ta kai yaran ga
mutuwa.
"Hujjojin da ke hannunmu zuwa karshen wannan
bincike namu, wadanda da su mu ka dogara
wajen shigo da wannan kara su ne;-
(Dan Allah kuyimin afuwa nangun ya yanke)
"Zan fara da gabatarwa da shari'a kaina". Ta ci
gaba, "Sunana Barista Hannatu, lauya mai zaman
kanta. Na dauki wannan bangaren ne na ba
wadda ake zargi kariya kasancewar har zuwa
yanzu babu wata kwakkwarar hujja ta zahiri da
ke nuna cewa, Zainab ita ta samar da wannan
alewar. Sannan ina kira ga shari'a da ta yi duba
da cewa, duk fa abin da a ka ce zargi a ke yi, bai
tabbata ba kenan, akwai bukatar samun tabbaci
tun kafin a shigo nan. Don haka ina fatan kotu ba
za ta damu da duk wadannan abubuwa ba tunda
an nuna ba a bincika an tabbatar ba. Idan kuwa
haka ne akwai bukatar shari'a ta yi kyakkyawan
duba ga ingantattun hujjojin da za a gabatar ma
ta domin tserewa da gudun afkawa ga dorawa
mara laifi, laifi. Na gode!" Ta koma ta zauna.
Duk da cewa wannan jawabin nata kusan bai
gamsar da kowa ba, da alama shi mai shari'a ya
gamsu. Za ka gane haka ne ta hanyar gyada kai
da ya yi, ya kuma duka ya yi yan rubuce-rubuce.
A hankali ya dago ya dubi Barista Garba Shehu,
"Shari'a ta baka dama ka fara gabatar da
shaidunka yanzu."
Garba ya mike ya fara takawa a hankali. "Da ya
ke shari'a ta amince zan fara gabatar da mutane
biyu a matsayin shaidar farko, amma daya bayan
daya. Mutanen kuwa su ne, Alhaji Sambo kanin
maigidan wadannan mata, uwa daya uba daya,
da kuma Alhaji Gali babban aminin mijin
wadannan mata. Amma da ya ke na ce daidai da
dai-dai, za mu soma da kanin magidancin."
Alhaji Sambo da ke sanye da manyan kaya
(Malum-malum) ya mike ya nufi mumbarin
shaida, ya shiga ya tsaya, aka rantsar da shi.
Garba ya isa gare shi, "Ko za ka iya tabbatarwa
da shari'a matsayinka ga Alhaji Basiru, mai gidan
wadannan matan?"
"Kwarai kuwa!" Ya ce ya na gyada kai.
"To za mu so hakan."
"Ni dai uwarmu daya, ubanmu daya." Ya fada a
takaice.
Garba ya gyada kai "Da kyau! Kasancewarka ka
na daga cikin mutanen da su ka tsinci kansu cikin
wannan falo yayin faruwar wannan al'amarin, ko
za ka iya sanar da mu yadda abin ya faru?"
"Tabbas zan iya". Ta ke ya zayyanewa kotu duk
yadda a ka yi har zuwa sa'ar da su ka dunguma
asibiti.
Garba ya nisa cikin gamsuwa "muna godiya."
Har ya yunkura da zummar sauka daga kan
mumbarin shaidar sai ya ga mai shari'a ya juya
ga Hannatu, "Ko ki na da bukatar tambaya?"
Ta gyada kai kana ta mike, ta nufi mumbari.
Bayan ta isa ta ce, "A matsayinka na wanda ya
ke cikin falon abin ya faru ko za ka iya sanar da
mu wanda Zainab ta dankawa wannan alewa
sa'ar da ta shigo falon?"
Ya gyada kai "Lallai kuwa".
"To wane ne?"
"Mujahid ta ba."
"Mujahid dan wane ne?" Ta bukata.
"Dan ta ne." ya amsa.
"Kenan mutum zai iya daukar gubar mutuwa ya
ba dan da ya haifa a cikinsa, musamman ma
uwa
da danta...?"
"Malama saurara!" Garba ya mike, "Ya mai
shari'a ina so kotu ta lura da cewa, wannan
tambaya da aka shigar yanzu ta sauka daga kan
asalin turbar da mu ke don kuwa me tambayar
ta
tambayi abin da ke cikin zuciya ne, kuma shi
sanin gaibu sai dai Allah, Lallai ya dace a duba,
wannan abin tsawatarwa ne."
Mai shari'a Muktar Kano ya dubi Hannatu gami
da tsawatar ma ta, da kar ta kuma irin wannan
tambayar.
"Na daina ranka ya dade." Hannatu ta ce kana ta
kuma mayar da dubanta ga Alhaji Sambo.
"Alhaji a lokacin da wannan al'amari ya faru an
ce Hajiya Rukayya ta na waje, haka ne?"
"A'a tana kicin dai." Ya gyara ma ta.
Ta gyada kai "Ma'ana dai ba ta falon ko?"
"Yaron nan mujahid ne ya fita da kukansa ya je
ya sanar ma ta. Shi ne ta taho a guje."
Ta gyada kai, "A lokacin ta taho ta namagana, ko
za ka iya tuna abin da take fada...?"
"Ya mai shari'a." Garba ya yi caraf ya cafe,
"Kamar yadda na sanar yanzu, wajibi ne kotu ta
dauki tsauraran matakai kan irin wadannan
tambayoyin domin kauracewa afkawa rudani."
Mai shari'a ya dubi Garba ya ce, "Ina so ka
fahimta cewa, ba kowace irin tambaya ce ta
sabawa doka ba, irin wannan tambayar akan
hanya ta ke, don haka kai ma ka kiyaye."
Barista Garba ya koma ya zauna cikin damuwa
ganin mai shari'ar ya ba Hannatu damar ci gaba.
Hannatu ta ci gaba, "To Alhaji za ka iya tuna
abin da ta ke fada sa'ar da ta nufo falon?"
Sai da ya yi dum na dan lokaci kana ya ce, "Na
tuno."
"Me ta ke cewa?"
"Cewa ta ke, Alhaji kar ku sha alewar nan, alewar
nan ba ta da kyau!"
Hannatu ta juya ga mai shari'a, ta ce, "Ya mai
shari'a lallai babu shakka ina so kotu ta lura ta
gano wasu sirrika daga cikin maganar baiwar
Allahn nan, don babu yadda za a yi kaza ta san
hanyar rafi, abin nufi babu yadda za a yi Hajiya
Rukayya da ba ta san komai a kan wannan alewa
ba, ta yi wannan furuci. Na gode!" Ta koma
wajen
zamanta ta zauna.
Garba ya mike "Shaida na gaba da za mu kira wo
kamar yadda mu ka ce, shi ne aminin Alhaji
Basiru wato Alhaji Gali."
Alhaji Gali ya hau mumbarin shaidar, bayan Alhaji
Sambo ya sauka. Garba ya isa gare shi.
"Zan so kai ma ka sanar da shari'a matsayinka
ga Alhaji Basiru, wato mai gidan wadannan
matan."
"Sunana Alhaji Gali." Ya soma da gabatar da
sunansa.
"Kuma ni babban amini ne ga Alhaji Basiru." "Ko
kai ma ka na cikin wadanda su ka riski
kawunansu a cikin wannan falop sa'ar da abin ya
faru."
Ya gyada kai "Hakika!"
"To me za ka ce mana game da faruwar wannan
abu?"
Ya gyada kai, kana ya soma zayya na abin da ya
faru. Ba su sami sabani ba, kusan abu guda su
ka fada shi da Alhaji Sambo. Bayan ya kammala
sai Garba ya yi masa wasu tambayoyi guda biyu,
kamar haka.
"Wato dai ya tabbata Zainab ta dauko wannan
alewa kenan?"
"Kuma a dakinta?"
"Babu ko shakka!"
"To madalla mun gode." Garba ya koma wajen
zamansa ya zauna.
Ganin ba ta taso ba ya sa mai shari'a Muktar
Yakub ya juya gare ta "Ki na da tambaya ne?"
Hannatu ta girgiza kai, "Babu yallabai!"
Yar hayaniya aka yi kadan, me yiwa ta samo asali
ne da tunanin mutanen na fara ganin gazawar
Hannatun.
Garba Ya mike, ya ce "Shaida na gaba da za mu
gabatar wanda ya zama shi ne mutum na farko
da ya halarci wannan gida bayan faruwar
al'amarin shi ne Likita Idris, wanda kuma dama
can likitan gidan ne."
Likita Idris ya fito, dan kakkaura ne haka fari, mai
sakakkiyar fuska.
Garba ya ce, "Likita zan so ka warware min zare
da abawa game da matsayinka a wannan gida,
da
kuma tsawon lokacin da ka dauka ka na yi musu
aiki."
Ya gyara murya, "Kamar dai yadda ya ke, a
gaskiya ni likita ne na musamman a wannan gida,
kuma tsawon shekaru goma kenan."
Garba ya gyada kai "Da kyau! Wato duk abin da
ya faru na game da rashin lafiya a gidan kai a ke
nemo wa kenan?"
"Haka ne."
"To sa'ar da wannan abu ya faru aka gayyato ka,
a ya ya ka riski abin?"
Sai da ya yi dan jim kana ya ce, "Ni dai lokacin
da na shiga falon yayin faruwar abin, na riski ita
uwargidan wato Hajiya Rukayya durkushe gaban
yayanta biyu, sai kuma Zainab, amaryar kenan,
durkushe a gaban mijinta, Alhaji Sambo wato
kanin Alhajin kenan da kuma aminin Alhajin wato
Alhaji Gali tsaye a kanta. Ganin hakan ni sai na
nufi gun Hajiya Rukayyar don ba ta tallafi."
"To ita Zainab din me ta ke yi ga Alhajin?"
"Ta nagwagwgada shi ne da irin abin gwajinmu
na likitoci."
"Hakan ya nuna ita ma likita ce kenan?"
"Kwarai kuwa likita ce."
Garba ya juya ga mai shari'a ya ce,
"Ya mai shari'a idan har shari'a za ta tsaya ta
fuskanci inda wadannan jawaban su ka sa gaba,
lallai za mu ga cewa akwai wata makarkashiya
cikin wannan al'amari wanda ya afku a ba-zato,
wanda za mu ga kiri-kiri Zainab ba ta damu da
yayan kishiyarta ba, ta mijinta ta ke, wanda
wannan kadai ya isa ya sa a fahimci cewa akwai
manufa ta son kisan gilla ga wadannan yara." Ya
yi godiya ya koma ya zauna.
Hannatu ta tako zuwa ga mumbarin da likita ke
kai. Ta dube shi, "Likita ko za ka iya sanar da
mu yadda aka yi ka sami labarin faruwar wannan
al'amari?"
"Eh! An sanar da ni ne ta waya."
"Wane ne ya sanar da kai?"
"Amarya ce".
"Wace ce amarya?"
"Zainab."
"Wadda a ke zargi kenan?"
"Eh!" ya amsa ta hanyar gyada kai.
"Ita ce ta yi ma waya, ta ce da kai me?"
"Ta ce don Allah na yi gaggawa na zo."
Ta nisa kana ta juya ga mai shari'a, "Ya mai
shari'a, idan mu ka yi la'akari da wannan za mu
fahimci cewa, babu yadda za a yi matar da ta yi
shirin aikata wannan abu da ake zarginta da shi
yanzu, ta yi tunanin sanar da kafar da za ta
bayar da taimakon gaggawa, don hakan na nuna
cewa a na son ceto rayukan wadannan yara,
musamman idan mu ka duba cewa ita ma likita
ce zata iya ba mijinta shi kadai kariya, idan har
zargin da a ke ya tabbata..."
Tun kafin ta karasa hayaniya ta soma fitowa jifa-
jifa, da alama jama'ar sun fahimci abin da
Hannatun ta ke nufi, kuma har wasunsu ma sun
fara shiga cikin tunanin abin. Bayan mai shari'a
ya tsawatar sai aka yi shiru.
Bayan saukar likita Idris daga kan mumbarin
shaidar, sai Garba ya mike, sai dai mikewar tasa
ta yanzu ba kamar ta baya ba.
"Kafin na kira shaida na gaba ina so na yi amfani
da wannan dama domin kira ga kotu da ta rika
dubawa ta nakuma bijirewa irin wadannan
sakarkarun tambayoyi da aka gabatar yanzu ko
don tsafta ce wannan shari'a." Ya dan yi shiru
kana ya ci gaba "Shaida na gaba da na ke son
gabatarwa shi ne jami'in bincike a kan kisan kai,
wanda kuma shi ne ya bi diddigin wannan
al'amari, wato Sifeto Habibu Hudu Darazo."
Sufeto Habibu ya mike ya shiga mumbarin shaida
ya tsaya. Garba Ya dube shi, "A matsayinka na
mutumin da wannan al'amari ke hannunka ta
fuskar bincike, ko za ka iya sanar da shari'a
sakamakon da kuka tattara?"
Daki-daki Sifeto Habibu ya yi bayanin game da
sakamakon bincikensu da kuma irin shaidun da
su ka samu har zuwa lokacin da su ka miko
karar ga kotu.
Garba ya yi masa godiya, ya koma wajensa ya
zauna. Hannatu ta mike ta nufi mumbari shaidar
da Sifeton ke tsaye, "Sifeto zan so na san lokacin
da ku ka isa gidan, abin nufi karfe nawa?"
"Karfe takwas mu ka ce za mu isa gidan, amma
saboda wani dan tsaiko da mu ka samu takwas
din ta dan gota."
"Yallabai kenan, saba lokacin bai sa kun samu
matsala ba wajen ganawa da duk wanda ya dace,
tunda watakila idan su ka ga lokacin ya gota za
su iya fidda rai da zuwanku?" Sifeto ya yi
murmushi, "Ba mu sami wannan
matsalar ba, sai dai..." Ya dan yi shiru gami da
dukar da kansa alamar tunani.
"Sai dai me?" Hannatu ta bukata ganin shirun
nasa na yunkurinsa tsawaita.
Ya dube ta, "Sai dai uwar gida da ba mu sami
damar ganawa da ita ba."
"Uwargida? Hajiya Rukayya kenan?"
"Eh, ita." Ya gyada kai.
"To me ya hana damar ganawar da ita?"
"Saboda ta yi barci lokacin..."
"Barci?" Ta nanata cikin mamaki. Ba ita kadai ba
ma kusan kowa a kotun sai da fuskarsa ta sauya,
har da shi mai shari'ar.
Ta juya ga mai shari'ar, "Ya mai shari'a lallai
wannan gagarumin al'amari ne, ko na ce
gagarumin sakaci ne da ya bar baya da kura,
wanda kuma kacokan zai iya sauya dukkan
sakamakon da jami'an su ka samu, domin kuwa
wadda su ka bari din ita ce ta farko da ya dace a
ce an gana da ita kuma ma abin tambaya ne a ce
wai matar da ta rasa yayanta biyu ta sami damar
barci. Don haka ina kira ga shari'a da ta shata
layi a karkashin wannan babban kuskure don
gudun kar a yi tsallen-badake a cikin wannan
shari'a. Na gode." Ta koma ta zauna.
A wannan karon ma sai da mai shari'a ya
tsawatar saboda hayaniya da ta sopma karfi.
Bayan an sarara ne mai shari'a ya dubi Garba
ganin bai taso ba.
"Garba ko shaidun sun kare ne?"
Ya mike "A'a ba su kare ba, yallabai. Yanzu zan
gabatar da shaida ta gaba wadda koken ta ne mu
ke dubawa a yanzu, kuma matar da a ka ci
amanarta wato Hajiya Rukayya."
Hajiya Rukayyar ta fito ta hau mumbari.
Garba ya dube ta, "Hajiya Zan so na ji ko lokacin
faruwar wannan al'amari, ki na cikin falon?"
T girgiza kai "Ba na ciki"
"To ke me ki ka sani kenan dangane da
al'amarin?"
"Ranka ya dade, ni ban san komai ba, kawai dai
ina cikin dakin girki sai na ga dan wajen amaryar
tawa ya zo ya na sanar da ni cewa wai ga..."
Shisshikar kuka ce ta hana ta karasawa.
"Sannu Hajiya Ki yi hakuri...kar ki yi kuka." Garba
ya shiga ba ta hakuri. Bayan ta sassauta, sai ya
juya ya koma ya zauna.
Hannatu ta mike, "Da farko in jajenta miki
wannan rashi, Hajiya Allah ya ji kansu."
"Amin." Ta amsa da kyar.
"Hajiya sa'ar da aka sanar da ke cewa ga abin da
ke faruwa, abin nufi lokacin da Mujahid ya kai
miki kara cewa an kwace masa alewarsa. Me ya
sa ki ka nufo falon a rikice?"
Fuskarta ce ta sauya lokaci guda. Ba ta yi
tsammanin wannan ta nacikin tambayar da za a
yi mata ba. Shiru ta yi na yan dakiku.
"Ba ki ce komai ba...ko kin taho ki kwatarwa
Mujahid din alewar ne..."
"Eh...e...ha...ka ne.." Ta ce cikin in ina ta
nagyada kai, gami da kifkifta idanu.
Hannatu ta yi murmushi, "To kuma me ya sa ki
ka taho ki na ambatar cewa kar su sha wannan
alewa ba ta da kyau?"
Yanzu ma shiru ta yi cikin rarraba idanu. Tsawon
dakiku goma ba ta yi magana ba, hakan ne ya
jawo hayaninya a cikin kotun. Hayaniyar da
jama'ar ke yi ta nuna mamakinsu ga faruwar
wannan al'amari. Bayan kotun ta yi shiru ta
hanyar tsawatarwa daga mai shari'a Mukhtar, sai
Garba ya mike jiki a sanyaye.
"Ya mai shari'a ba zan taba amincewa da
wannan soki-burutsun tambayioyi ba. Sannan ina
kira ga shari'a da ta bada umarnin a sassautawa
wannan mata domin a halin yanzu ta na fama da
tunanin makokin yayanta don gudun kar a tilasta
ta ta amsa abin da ba ta yi ba." ya koma ya
zauna.
Mai shari'a ya dube shi, "Kotu ba za ta iya amsa
wannan kira naka ba domin kuwa ya nayin mai
amsar tambayar, ya nayi ne da ke da rufa-rufa a
ciki, saboda haka akwai bukatar a kwalkwaleshi
tas domin ketare zalunci a cikin wannan shari'a."
Ya juya ga Hannatu ya ba ta umarnin ta ci gaba.
Hannatu ta kuma murmushi bayan ta dubi Hajiya
"Hajiya ba ki fadi dalilin da ya sa ki ka ambaci
waccan kalmar ba, ko daman kin san da alewar?"
"A'a...ban...san..da ita ba...kawai dai..." Ta kasa
karasawa, ta juya kallonta ga Barista Garba da
tuni kansa ya fara daukar zafi.
"Kawai me?" Hannatu ta dawo da hankalinta gare
ta.
Yanzu duk idanun da ke kotun kallon ta su ke
cikin mamaki.
"Hajiya ya kamata ki amsa wannan tambaya
domin ki na batawa shari'a lokaci". Mai shari'a
Mukhtar ne ya fada.
Ta yi ajiyar zuciya "Saboda alewar ba saya aka yi
ba."
Idanun da yawa daga cikin mutanen ne su ka
kara girma don mamaki.
"kamar ya ya ba saya aka yi ba, mu na so ki
fayya ce ma na.
"Ba...ba ni ce na sa..ya ba.. Wata...kawata...ce
Baraka...ko da ya ke na saya mu...musu alewa a
makaranta...uhn...uhn..." Ta kasa ci gaba.
Hayaniya ta kaure a kotun kamar kasuwa, wasu
har mikewa su ka yi don mamaki. Bayan an
tsawatar Barista Hannatu ta dubi Hajiaya
Rukayya ta ce, "Hajiya, yanzu dai ya tabbata ke
ce ki ka samar da wannan alewa kenan?"
Ba ta yi magana ba.
Hannatu ta juya ga alkali, "Ya mai shari'a kamar
yadda na sanar tun a farko, cewa wannan shari'a
tabbatattun shaida ne kadai ke da muhimmanci
wajen gano gaskiyar wannan al'amari, to wannan
haka ya ke, domin kuwa idan mu ka duba a
yanzu bisa wannan tabbatarwa da wannan mata
ta yi da bakin..."
"Ba zan taba amincewa da wannan ba." Garba ya
mike, "Ya mai shri'a babu wata hujja a yanzu da
za ta
tabbatar da a bin da Hannatu ta ke shirin fada
domin kuwa tun farko sai da na ja hankalin
shari'a a kan ta tsawatar da a sassauta wajen
yiwa wannan mata tsauraran tambayoyi don
gudun kar a tilasta ta fadi abin da ba ta yi ba,
kamar yadda a ka yi mata yanzu. Sannan daga
karshe ina rokon shari'a da ta daga gabatar da
wannan kara saboda dalilanmu na son binciko
wasu kwararan hujjojin da za su tabbatar da
gaskiyarmu, kuma kafin lokacin wannan baiwar
Allah ta dan huce."
Mai shari'a ya dubi Hannatu da ke ta faman
murmushi ya ce, "Mene ne ra'ayinki dangane da
rokonsa, ki na da ja?"
"E, to ranka ya dade tun da har an samu tsaiko
da dalilin gazawa daga abokin karawar tawa, zan
iya amincewa, amma akwai wata alfarma da na
ke bukata shari'a ta yi min. Lallai ya zama wajibi
shari'a ta nemo wannan mata Baraka da Hajiya
Rukayya ta ambata ta hanyar tuhumar ita
Hajiyar, don kuwa ba yanzu ba ne ta fara
ambatar sunanta, ta soma ambatar sunan matar
ne tun sa'ar da su ke a asibiti, saboda haka babu
ko tantama nemo matar gagarumin abu ne da ya
ke da matukar amfani."
Mai shari'a ya dukar da kansa ya yi yan rubuce-
rubuce, kana ya dago, "Mun ji wannan kira naki
Hannatu kuma lallai za mu aikata. Sannan mun
daga wannan zama zuwa ranar Alhamis ashirin
da hudu kennan ga wannan watan, a matsayin
ranar da za mu ci gaba da sauraron wannan
shari'a.
Da wannan kotun ta tashi. 'yan sanda su ka
kuma tusa keyar Zainab zuwa cikin bakar motar
su ka tafi da ita, yayin da dokacin jama'ar da su
ka sami sauyin ra'ayi daga zargin na zainab su
ka bi motar da kallo suna cewa,
"Allah Sarki, baiwar Allah, Allah ya kubutar da
ke."
***
Kashe gari da safe Hannatu ta nufi makarantar
"Sasif da burin samun dan saurayi mai shagon
sayar da kayan tsotse-tsotse, Habu mai shago.
Tafiyar tata kuwa ta yi nasara, domin lokacin da
ta isa makarantar dan saurayin na zaune cikin sa
rai da ganin wanda zai zo ya yi masa ciniki, don
haka ta na tsayawa a karamar motarta kirar
Toyota Starlet, ya zubawa motar idanu.
Lokacin da Hannatu ta kashe motar ta turo kofar
ta fito, sai ya yi wata nannauyar ajiyar zuciya,
kana ya ce, "Kai, ka ga wata tsaleliya, tsada!
Allah ya yi halitta a nan. Tsantsari!"
Amma ko da ya fuskanci ta nufo shi sai ya yi
sauri ya dauke kansa daga kallon ta a kokarina
na kare mutuncinsa, don ba zai taba mantawa
ba,
akwai wata yarinya kyakkyawa da ya taba kallo
ta tambaye shi "Mene ne ya ke kallon ta?"
"Assalamu alaika." Hannatu ta yi masa sallama
sa'ar da ta isa gare shi.
"Wa'alaikis salam!" Habu mai kanti ya dawo da
hankalinsa gare ta, "Sannu da zuwa."
"Yauwa sannun ka, ya gari?"
"lafiya sumul, ya hutu?"
Ta yi yar dariya, "Malam, hutu ai sai ku."
"Hajiya wane mu?"
"Ba sunana Hajiya ba, sunana Hannatu."
Yayi dariya "Ai idan na ce Hajiya ban yi laifi ba."
Su ka yi yar dariya su dukansu.
"Malam don Allah wata bukata ce ta..."
"Ba sunana Malam ba, sunana Habu mai kanti
kuma ki na iya kirana da "Harka".
Ta yi murmushi "To Habu mai kanti kuma Harka,
ina da bukatar yin wata magana da kai."
"Ni?" Ya bukata cikin mamaki.
"Kwarai, kai"
"To Bismillah, wace magana ce?"
"Dan samar mana abin zama mana?" Ta ce ta na
duban sa.
Ya waiga "Ga wani benci can mu karasa gare
shi." Ya nuna wani benci da ke ajiye can gefen
gindin wata bishiya. Su ka nufi bencin fuskar dan
saurayin cike da mamaki. A lokaci guda kuma
zuciyarsa na ta saka masa cewa.
"Lallai ka yi sa'a ka sami kyakkyawa, idan ta ce
ta na son ka kar ka kuskura ka yi sanya don
auren irin wadannan na da ribobi. Ka ga na farko
dai ko ba komai fuskarta da kirar jikinta ta shiga
taro ce. Na biyu kuma daga duk inda ta fito yar
mai abin hannunsa ce, ka ga shi kenan ka sami
auren jari."
Bayan sun isa ga bencin sun zauna sai Hannatu
ta shiga gabatar ma sa da kanta, sannan daga
baya sai ta shiga tambayarsa, "Habu don Allah
ko za ka iya tuna adadin mutanen da su ka zo
sayayya kantinka daga makon da ya wuce zuwa
yau din nan? Misali daga ranar Litinin sha biyu
ga watan sha biyun nan har zuwa yau?"
"Eh...gaskiya ba zan iya tunawa ba, amma da ya
ke ina rubuta duk abin da na sayar ba mamaki
na
gane."
"To idan ka rubuta abin da ka sayar kana rubuta
sunan wanda ka sayarwa ne?"
"A'a"
"To, ya za a yi ka gane?"
"Wani lokaci idan na dauko littafin ina dubawa,
zuciyata na kokarin tuna min kamannin mutumin
da ya yi sayayyar, in dai ba lokaci guda mutane
daban-daban su ka zo ba."
Taq gyada kai "To yanzu za ka iya dauko littafin
kenan?"
"Me zai hana." Ya mike ya nufi kantin nasa.
Ta bi shi da kallo har sa'ar da ya shiga cikin
kantin ya dauko littafin, da sauri ya kuma nufowa
wajenta, "Kin ga littafin." Ya mika ma ta bayan ya
zauna.
Ta kuma mayar ma sa, "To bude ka duba mana,
a ranar sha biyu ga wannan watan su wane ne
su ka zo su ka yi sayayya?"
Ya karba ya fara budewa. Da ya zo shafin ya
tsaya, "Kin ga mutum biyar ne kawai su ka yi
siyayyar a ranar, da ya ke ban jima ba na rufe
saboda tafiya da zan yi a ranar." Ta dan leka ta
dubi littafin, "To za ka iya tuna mutanen?"
"Da wa-da wa kenan?" Ta bukata a kagauce.
"Kin ga dai wannan Naira hamsin din malami ne
a nan makarantar, malam Ibrahim
Mu'azzam ya sayi sabulu guda biyu GIV, wannan
kuma Naira dari da Naira sha
biyar din wata mata ce da ta kawo yara cikin
wata mota Lexus, ta sayawa yaran
alewa da biskit, wanan su ne kawai zan iya
tunawa."
Hannatu ta dube shi ido da ido, "Matar da ka ce
ta zo da yara ya ya take?"
"Su uku ne, mata biyu namiji daya. Abin da ya sa
na tuna hakan, bana mantawa,
biskit uku ta saya alewa biyu har na tuna ma ta
cewa alewa uku ya kamata ta
saya amma sai ta ce dai biyu zan kawo ma ta. To
bayan na kawo ne da ta raba
alewar yaron namijin bai samu ba, har zai yi ma
ta kuka sai ta bude yar jakarta ta
dauko ma sa wata alewar."
Hannatu ta nisa bayan ya ida. Shakka babu
yanzu ta sami abin da take so kuma
ta nada tabbacin Hajiya Rukayya ce, saura da
me?
Ta dube shi "Habu za ka iya tuna kalar biskit din
da alewar da ta saya?"
"Sosai, ai ga sunan a rubuce, alewar "NANY" ce,
shi kuma biskit din "Shortcake'
ne".
Ta gyada kai "Na gode, Habu yanzu saura
taimakon da na ce za ka yi min."
ya dube ta, "Fadi ina jin ki."
"So na ke dan Allah ranar Alhamis ka halarci kotu
dan bada wadannan shaidu
domin..." Ya daga ma ta hannu.
"Wace kotu ce?"
"Arewa majistiri"
Ya yi dariya, "Kin ce da ke za a tsaya ko?"
"Kwarai kuwa."
"To kar ki damu, idan Allah ya so zan zo to sai
dai ni ma da bukatata gare ki
bayan kammala shari'ar." Ya ce ya na dariya.
Ta kalle shi, bayan ta mike tsaye "Mece ce
bukatar taka?"
"Wallahi kaunarki nake yi, yar kyakkyawa."
Zuciyarsa ce ta fada. Amma a fili sai
ya ce, "Ki dai bari sai ranar."
"To Allah ya kai mu," Ta ce. Ya taka ma ta, su na
hira har gindin motarta. Ta
bude ta shiga, ta tashe ta, ta tuka ta bar
makarantar cikin murna da ganin cewa
kawarta za ta kubuta daga zargin da a ke yi ma
ta.
Shi kuwa dan saurayi Habu mai kanti ya bi motar
da kallo yana ta murna ya sami
budurwa kyakkyawa.
ZAMAN KOTU NA BIYU
A yau ma kotin ta arewa tak ta ke taf da jama'a,
kusan ta fi zamanta na farko ma
cika. Meyiwa hakan na da alaka da bazuwar da
shari'ar ta yi ta hanyar mutanen
da su ka halarci zamanta a karo na farko. Lokacin
da lauyoyin su ka shigo kotun
sai jama'a su ka shiga nuna su wasu da zunde,
musamman ma Barista Hannatu
da su ke ganin ta nuna bajinta a zaman farko.
Kafin Barista Hannatu ta zauna sai da ta dubi
jama'ar, ta dubi bangaren da Zainab
ta ke ta yi ma ta murmushi ita ma Zainab da ke
dauke cikin sarka ta mayar mata
da murmushin da kyar, kana Hannatu ta zauna.
Zamanta ke da wuya sai ta hango
cikin jama'ar ana dago ma ta hannu, ko da ta
lura da kyau sai ta ga ashe Habu
mai kanti ne. Ta daga masa hannu ita ma cikin
fara'a don ta yi matukar jin dadin
ganin sa. Shi kuma ganin ta dago masa hannu sai
ya yi ajiyar zuciya kana ya ce,
cikin zuciyarsa.
"Kai, Allah fa ya yi hallita a nan. Ni idan wannan
tsaleliyar za ta amince ta aure ni,
ai zan iya amincewa a tsire min idanuwana duka
na daina ganin komai, tunda ina
tare da kyakkyawa karshen kyau."
Da misalin karfe goma da yan dakiku mai shari'a
Mukhtar Kano ya shigo cikin
dakin shari'ar.
Kamar yadda ya ke, jama'a duk su ka mike cikin
girmamawa. Bayan mai shari'a
ya yi rankwafawar da ya saba cikin girmama
jama'ar, sai suma su ka rankwafa a
girmame, ya zauna kan kujerarsa kana kowa ya
zauna. Kotun ta yi tsit.
Bayan kotun ta samu nutsuwa, mai gabatar da
shari'a Furoskito Nura Salihu ya
mike hannunsa rike da takardu.
"Yau ranar Alhamis ashirin da uku ga watan sha
biyu, ita ce ranar da Shari'a ta
ajiye don ci gaba da sauraron wannan kara,
wadda ake tuhumar Zainab Ilyas
amaryar Alhaji Basiru da yiwa yayan kishiyarta
kisan gilla". Ya rankwafa
girmamawa ka na ya kuma tsawatarwar da mai
shari'a Mukhtar Kano ya yi, sai ya
dubi Hannatu, "Kafin mu mika damar ci gaba da
gabatar da shaidu ga Barista
Garba ko ki na da wani abin da za ki ce?"
Hannatu ta girgiza kai "Babu Yallabai. Sai dai ina
so na yi tambaya ga shari'a ko
ta samo wannan mata, Baraka?"
Mai shari'a ya gyada kai "Kwarai an samo ta, shi
kenan?" Ya bukata.
"Ranka ya dade, shi kenan." Hannatu ta ce
Mai shari'a ya dubi Garba "Bismillah".
Garba ya mike, "Zan so na yi amfani da wannan
dama, na yi kira ga shari'a kafin
na ci gaba da gabatar da kwararan shaidun
nawa. Babu shakka ya dace akwai
kuma soyuwar a ce shari'a ta gane cewa, ba
kowane dan Adam ne ke iya magana
ko amsa tambaya cikin jama'a ba ba tare da ya
yi rawar baki ba. Don haka ina
kira ga shari'a da kar ta yi la'akari da gaza amsa
tambayar da shaidun da zan
gabatar za su.."
"Ina da ja!" Hannatu ta mike "Ya zama wajibi na
kalubalanci wannan sharhi da
Garba ya yi. Ya mai shari'a babu yadda za a yi
gumi ya karyowa mai gaskiya a
cikin ruwa. Abin da nake nufi shi ne, ba zai taba
yiwuwa a ce mutumin da ke da
gaskiya ya gaza amsa tambayar da za a yi ma sa
ko ya yi rawar baki yayin amsa
tambaya ba, matukar ba haka halittarsa ta ke ba.
"Don haka ina kira ga shari'a da ta yi watsi da
wannan kira don babu wata fa'ida a cikinsa." Ta
koma ta zauna.
Garba ya yi murmushin karfin hali, "Shaida na
farko da nake so na gabatar a yau shi ne direban
gidan Alhaji Basirun, wato Lukman."
Lukman ya fito ya hau mumbarin shaida.
Garba ya dube shi "Lukman kai ne direban gidan
Alhaji Basiru ko?"
"Haka ne." Ya amsa.
"Kai yara da dauko su ne kawai aikinka a gidan?"
Ya gyada kai "Haka ne."
"A ranar litinin sha biyu ga wata kai ka dauko
yara daga makaranta?"
"Eh, ni ne."
"Shin ko ka ga wani abu a tare da yaran sa'ar da
ka je daukop su a makarantar, abin nufi na
dangane da ci ko sha?"
"A'a." Ya girgiza kai.
"Kuma ba su fada maka cewa akwai makamancin
wannan abu tare da su ba, har sa'ar da ka kai
su
gida?"
Ya girgiza kai, "Ba su fada ba."
Garba ya yi ma sa godiya ya koma nya zauna.
Hannatu ta mike "Lukman zan so na san wanda
ya kai wannan yaran makaranta a wannan rana".
Sai da ya dan jinkirta kadan, kafin ya ce
wace Hajiya kenan?"
"Hajiya ce."
"Hajiya Rukayya."
"Daman ita ta ke kai su?"
"A'a... " ya girgiza kai, "Ni ne ke kai su".
"To, menene ya sa ta kai su a wannan rana?"
"Saboda bani da lafiya." Ya amsa kai tsaye.
"To, ba ka da lafiya, wa ya je ya dauko su da
rana?"
"Ni...ne?"
"Hakan na nufin ka samu sauki kenan?"
"Eh." ya amsa da kyar gami da gyada kai.
"Dangane da gurbin kwanan motocin gidan zan so
na ji, dukkansu su na kwana gida ne ko akwai
ma su kwana a wajenka?"
"A'a, duk a gidan su ke kwana, babu mai kwana
a
wajena." Sai bayan ya amsa ne ya gane cewa ya
yi kuskure, domin irin tambayar da ta yi ma sa
ya kasa amsawa, ita ta ke shirin yi ma sa yanzu.
"To, idan haka ne me ya sa a wannan rana ka
tafi da mota gida? Ko daman ka san za ka yi
rashin lafiya, kuma da rana za ka samu sauki?"
Lukman ya hadiyi yawu da kyar, "Motar ta kwana
wajena ne saboda..." ya yi shiru ya na kifkkifta
idanu, kamar kwado.
"Saboda me?" Hannatu ta dawo da hankalisa
gare ta.
Ya na rawar baki ya ce, "Saboda Hajiya ce ta ce
na tafi da ita."
"Wace Hajiyar?"
"Hajiya Rukayya." Ba shi da zabi ya zama wajibi
ya fada.
Idanun Hajiya Rukayya su ka dada girma, ta dafe
krji, alamun fargaba da mamaki.
Ta mike tsaye "Wace Hajiyar, Ni?" Ta ambata
cikin karaji, wanda hakan shi ya ja hankulan
daukacin mutanen dake kotun zuwa gare ta.
Ta juya kallonta ga mai shari'a. Ta soma rantse-
rantse, "Alkali! Na rantse da Allah...wallahi karya
ya ke yi min. Ni ban fada ma sa ya ta..."
Buga gudamar da mai shari'a Mukhtar ya yi ne
ta katse ta, tare da guna-gunin da jama'a su ka
soma.
"Zauna Hajiya!" Mai shari'a ya yi ma ta tsawa,
"Kar ki kuma magana in dai ba tambayar ki a ka
yi ba. Idan ba haka ba za ki fuskanci fushin
shari'a." Ya gargade ta.
Jama'a su ka kuma mayar da hankalinsu ga
Hannatu da Lukman don jin mafadar wannan abu
da ya soma ba su mamaki, ganin mai shari'a ya
umarce ta da ta ci gaba da yin tambayoyinta.
"Saki jikin ka malam Lukman, ko za ka sanar da
mu dalilin da ya sa a wannan rana ita Hajiyar ta
ce ka tafi da motar gida?"
Ya girgiza kai, "A'a, wallahi ni ma ban san dalili
ba. Ni ma na yi matukar mamaki,tunda tun da
na
soma tuki a gidan hakan ba ta taba faruwa ba."
Da alama ya amsa kiran na Hannatu, na ya saki
jikinsa tunda yanzu murya ba ta rawa.
Kuma ko washe gari ba ka tambaye ta ba?"
Ya girgiza kai, "Gaskiya ban tambaye ta ba
saboda..."
Ya yi shiru.
"Saboda me?"
"Saboda ta ba ni kudi. A yanzu ya kudiri aniyar
fadar gaskiya, don haka ba ya fargabar duk abin
da zai biyo baya.
Mamaki ne ya kara bayyana a fuskokin jama'ar,
kana hayaniya ta biyo baya.
Mai shari'a ya tsawatar. Bayan an yi shiru,
Hannatu ta ci gaba, "Kenan ya tabbata a wannan
lokaci akwai abin da ta ke kullawa, wanda daga
bisani shi ya yi sanadiyar ya yanta ko?"
"Kin ga saurara Hannatu." Garba ya katse ta a
fusace, "Ya mai shari'a ba zan taba amincewa da
irin wannan tursasawa ba. Don kuwa ta
nakokarin wanda ta ke yi wa tambayar ya
tabbatar ma ta da abin da bai sani ba. Lallai
wannan ya kauce layin da mu ke kai, ya dace a
tsawatar ma ta."
Mai shari'a ya tsawatar ga Hannatu. Ta yi
godiya, sannan ta koma wajen zamanta, fuskarta
cike da annuri, musamman ma ganin yadda ta
fuskanci kan yan kallo ya fara wayewa.
Garba ya ce, "Zan gabatar da shaida na gaba
kuma na karshe, wanda kuma nake matukar
fatan
ganin cewa daga kansa kotu za ta fahimci
gaskiya, ta kuma yanke hukunci ga wannan mata
mara amana. Wannan mutum shi ne mai gadin
gidan Alhajin." Duk da cewa jikinsa a sanyaye ya
ke yanzu, a muryarsa ya na kokari domin ba ta
sanyaya ba.
Maigadi Bukar ya hau mumbarin shaida.
Garba ya dube shi, "Malam Bukar mene ne
aikinka a wannan gida?"
"Gadi nake yi." Ya amsa kai tsaye.
"Kullum kai ne a bakin kofar kenan?"
"E, kwarai."
"A ranar da wannan al'amari ya faru ko ka ga
Hajiya Rukayya ta fita da mota, abin nufi ta tafi
kai yara makaranta?"
Ya girgiza kai "Gaskiya ban gani ba...ai bama ita
ce ke kai yara makarantata ba."
Garba ya gyada kai "Na gode." ya juya ga mai
shari'a"
(Matsala akasamu anan wacca badan itaba datini
nagama littafin,amma saidai nanemi afuwa dan
batawarwaru bakidayaba) "Abu na farko da za
mu lura da shi shi ne, hana
Lukman direba zuwa kai yaran makaranta da
kuma mallaka masa mota ta kwana a hannunsa
da zummar idan rana ta yi ya je ya dauko yaran,
bugu da kari da kudin da ta ba shi.
"Abu na biyu kuma hikimar aiken maigadi don
kar
ya ga sa'ar da ta fita zuwa kai yara makaranta.
Abu na karshe, alewa biyu da ta saya wajen
Habu
mai kanti, a maimakon uku wanda hakan ya
nuna
kiri-kiri ta tanadi waccan muguwar alewa kamar
yadda shi Habu ya ce ya ga ma sa'ar da ta
dauko alewar daga jakarta. Kuma idan mu ka
lura
da bawon wannan alewa mai guba ya bambanta
da wadda Hajiyar ta saya."
Hannatu ta gabatar da bawon alewar ga mai
shari'a kowa ya tabbatar ba iri daya ba ne da
wanda Hajiya Rukayya ta saya a wajen Habu.
Bayan an tabbatar ta ci gaba, "Daga karshe ina
kira ga shari'a da ta kula da wadannan dalilai da
su ka kama Hajiya Rukayya da yunkurin kashe
dan kishiyarta wanda daga bisani reshe ya juye
da mujiya." Hannatu ta koma ta zauna. Bayan
yan rubuce-rubuce da mai shari'a ya yi sai ya
juya kallonsa ga Barista Garba.
"Ko kana da abin cewa?"
Ya girgiza kai a sanyaye, "Babu ranka ya dade."
Har yanzu akwai guna-gunin jama'a.
Hannatu ta mike, "Ya mai shari'a zan so shari'a
ta ba ni dama na kirawo mace ta karshe wadda
na ke son na yiwa yan tambayoyi, wato Baraka."
Baraka ta hau mumbarin shaida ta tsaya. Kallo
daya za ka yi ma ta ka tabbatar ce gaba daya a
tsorace ta ke, kamar ace arr! Ta tsere. Sai
rarraba idanu take. Wannan ya nayi na Baraka ya
yi matukar yi wa Hannatu dadi, domin ta san dai
ko ba Komai Barakar ba za ta wahalar ba.
Hannatu ta dube ta, "Baraka mene ne tsakaninku
da Hajiya Rukayya?"
"Kawatace." Ta amsa a takaice.
"Tsawon wane lokaci?"
"Tun muna kanana"
"Tun daga wancan lokacin har zuwa yanzu ku na
tare?"
"E, muna tare a zuciya, amma mun dade ba mu
hadu ba." Kai tsaye kuma a takaice ta ke ba ta
amsar.
"Me ya sa?"
"Saboda mun tashi mun kma jigawa, tsawon
shekaru."
"Kun jima ba ku ga juna ba sai a yan makonni
biyu da su ka shude, haka ne?"
"Eh, haka ne."
"Mene ne ya kawo ki?"
"Ziyara na kawo gurin irinsu kawayena, da kuma
sauran yan uwa."
"Wato daga can ki ka taho ma ta da alewar me
guba da ta hallaka yayanta..."
"Wannan tambayar ba ta dace ba." Garba ya
katse ta bayan ya mike tsaye da hanzari. Sannan
ya juya ga mai shari'a, "Ya mai shari'a, ya
kamata fa a lura, Hannatu na amfani da wasu
irin
tambayoyi da ba sa kan la..."
"Ya isa Garba." Mai shari' ya katse shi,
"Tambayoyinta su na kan layi." Ya juya gare ta,
"Ki na iya ci gaba Hannatu."
Hannatu ta yi murmushi sannan ta kuma
maimaita tambayar ga Baraka, "Wato daga can ki
ka taho mata da alewar me guba da ta hallaka
yayanta..."
"Ni!" Ta katse Hannatu, "Wallahi bani ba ce." Ta
dubi bigiren da Hajiya Rukayya ta ke "Hajiya ke
ce ki ka ce ni na kawo miki wannan alewar?" A
rikice ta kuma mayar da dubanta ga Hannatu
"Wallahi tallahi ba ni na bata da hannuna ba. Ni
dai na san na raka..." Ta yi shiru saboda wani
abu da ya shiga zuciyarta.
"Kin san kin raka ta ina?" Hannatu ta bukata da
sauri. Idan ba ta fada ba ta san ita za ta kwana
a ciki.
Bakinta na rawa ta ce, "Na san ni na...ra...ka ta
ta karbo...alewar..."
Wani sabon ya nayi ne ya bayyana a fuskokin
daukacin ma su zaman shaidar, ciki har da mai
shari'ar. Yanzu idanunsu gaba daya ya na kan
Barakar.
"A ina ku ka karbo alewar?"
Ta soma kuka, "A wajen wani babban boka."
shi kenan ta bayyana. Hayaniya ta kuma kaurewa
a wannan karon shi kansa mai shari'ar kasa
tsawatarwa ya yi akan kari saboda mamaki. Sai
da aka samu tsawon lokaci kana da kyar ya
dakatar da hayaniyar.
Hannatu ta dubi mai shari'a, "A yanzu babu
bukatar na tsawaita jawabi domin gaskiya ta
bayyana, sai dai kira biyu da zan yi ga shari'a shi
ne, lallai ya wajaba ta hukunta Hajiya Rukayya da
kawarta Baraka hukunci mai tsauri don gudun
kada irin wannan ta kuma faruwa a gaba, donin
zamansu cikin jama'a haka sakaka hadari ne.
Haka nan kuma tilas ne shari'a ta hukunta duk
wanda ya ke da sa hannu cikin wannan shiri don
ya zama a gaba ya kiyaye don samun kyautuwar
al'umma. Kira na biyu, ina neman shari'a da ta
tirsasa Hajiya Rukayya ta biya Zainab diyar kudi
Naira Miliyan daya, don yunkurin bata ma ta
suna
da ta yi ta hanyar makala ma ta abin da ba ita ta
yi ba...bugu da kari da zaman da ta sa ta yi na
tsawon kwanaki a gidan horo. Daga karshe ina
addu'a ga duk matar da ta ke tare da kishiya,
Allah ya kiyaye ta kar a kulla ma ta sharin da zai
kai ta cikin wahalar da Zainab ta shiga, kwana
goma sha daya a 'Women Detention Centre'
ma'ana "Gidan horo na mata"
Kusan gaba daya kotun aka tallafawa addu'ar
Hannatu da "Amin". Ta yi godiya ta koma ta
zauna.
A yanzu dai Barista Garba ya yi shiru cikin tunani
da jimami gami da nadamar tsayawar da ya yi
wa Hajiya Rukayya kasancewar ta ba shi abin a
rufe. Ya yi tagumi hannu bibbiyu ya na jiran jin
hukuncin da mai shari'a zai yanke.
Hajiya Rukayya da Baraka da duk yan uwanta
kuwa babu abin da su ke yi sai kuka. Ba tare da
tsawaitawa ba ya yi bayani game da
duk hojjoji da shaidun da lauyoyin biyu su ka
gabatar. Bayan ya kammala sai ya fara bayar da
sakamako shari'ar kamar haka:-
"...Bisa dogaro ga duk wadannan hojjoji da
shaidu
da aka gabatar, shari'a ta tankade tsaf, kuma
daga karshe ta wanke wadda a ke zargi, wato
Zainab, ta kuma sake ta, bisa dogaro da doka
mai lamba 103, sashe na 119, sakin layi na biyu,
cikin baka. Kana ta zartar da hukuncin daurin rai
da rai ga Hajiya Rukayya bisa laifin da ta aikata
na zama silar kashe yayanta biyu...Da kuma
biyan Naira miliyan daya ga Zainab kamar yadda
lauyarta ta bukata, bisa dogaro da doka ta 99,
sashe na 121. Sakin layi na uku..."
Ihun da Hajiya Rukayya ta kurma ne ya katse mai
shari'ar, lokaci guda kuma ta sulale ta fadi kasa
sumammiya. Bayan yan sanda sun yi waje da ita
bisa umarnin alkali, sai ya ci gaba, "Haka kuma
Shari'a ta yanke hukuncin daurin shekaru goma
ga Baraka ba tare da tara ba, bisa laifin hada kai
don yunkurin aikata kisan kai. Shi kuwa Lukman,
kotu ya yanke ma sa hukuncin daurin shekara
guda bisa karbar cin hanci, amma shi zai iya
biyan tara ta Naira dubi hamsin...Wadannan
kuma mun yi duba ne ga doka mai lamba 69,
sashe na 173, sakin layi na farko, cikin baka."
Da wannan mu ka kawo karshen wannan
shari'a."
Ya rufe littafinsa ya mike. Duk jama'a su ka
mike.
Ita ma Baraka da Lukman su na kurma uban
kuka, har da kururuwa, yan sanda su ka yi awon
gaba da su.
BAYAN MAKO GUDA DA SHARI'A
Karfe tara na safiya wannan rana ta Alhamis a ka
sallamo Alhaji Basiru daga asibiti. Murna a wajen
Zainab ba a cewa komai.
Koda isowarsa gida jama'a su ka rika zuwa su na
yi ma sa jaje gami da ta'aziyyar rashin yayansa.
Bayan komai ya natsa, sahun jama'a ya dauke
daga zuwa yin jaje da gaisuwa, da karfe hudu na
yammacin wannan rana sai Alhaji Basiru ya
gayyaci matarsa dakinsa saboda wani zama da
za su yi, zaman da ya kira shi da zaman
shawara.
Da godiya ga Allah (S.W.T.) ya soma, bisa
ketarar da shi da ya yi daga wannan mummunan
hadari, kana ya ci gaba da cewa, "Zainab a farko,
bayan godiya ga Mai duka, ina mika jinjina gare ki
bisa namijin kokarin da ki ka yi wajen jure duk
abin da Hajiya ta ke mi ki.
Lallai kin isa jinjina, ya kuma dace da ma ga
kowace mace ta rike abubuwa hudu wadanda su
ne ki ka rike har ki ka kai wannan matsayi. Allah
ya saka mi ki da alkhairi."
"Amin." Ta amsa murya a sanyaye.
Shiru na dan lokaci babu wanda ya yi magana.
Zainab ta cira kai ta dubi Alhaji Basiru bayan ta
nisa,
"Alhaji." Ta kira sunan a nutse.
Ya dago kai ya dube ta, "Na'am amarya."
Ta dukar da kai cikin jin kunya ta ce, "Alhaji har
yanzu ban fita daga amarci ba? Shekaru nawa..."
"Har yanzu ba ki bar matsayin wannan suna ba
tunda ban yi wani auren ba, bayan naki."
Su ka yi dariya gaba daya.
"Me ki ke so ki ce ne?" Ya tambaya bayan sun
tsagaita da dariyar.
Ta yi murmushi, "Alhaji ina son sanin abubuwa
guda hudun nan da ka ce ya dace kowace mace
ta rike."
Shi ma ya yi murmushi, "Ai ke kin rike su shi ya
sa har yanzu ki ke zaune daraf a mukamin da
babu kamar ke a cikin zuciyata. Kuma duk macen
ma da ta rike su to babu shakka za ta zama
sarauniya a cikin zuciyar mijinta. Sai ta fi komai
soyuwa a zuciyarsa. Kai! Har ya ji cewa ma zai
iya bayar da ransa saboda ita."
Zainab ta numfasa, "Maigida ai ka san kogi bai ki
dadi ba. Ina so ka kara sanar da ni su don na
kara kankame su, don Wallahi ba na son abin da
zai bata ma ka rai ko kadan." Ta sunkuyar da kai
kasa.
Alhaji Basiru ya nisa, "Kina da gaskiya amaryata."
ya daga yan yatsunsa hudu, "Wadannan
abubuwa
guda hudu su ne; Hakuri da Biyayya da juriya da
kuma Gaskiya. Kin ga dai Hakuri shi ne, kawar da
kai da sanya dangana ga abin da aka yi ma ko
da ya bata ma ka rai. Juriya kuma ita ce, ci gaba
da jajirce wa a kan abin da ka ke yi mai kyau
komai tsangwama, Biyayya kuwa, bi da yarda da
abin da aka san bai saba wa Allah ba, don
farantawa miji rai. Gaskiya kuma, tsaya wa a kan
abin da ka san an yi ba tare da kaucewa ba, da
kuma yarda da abin da aka sanar da kai na game
da kuskure don gyara, komai dacinsa. Don akwai
Hadisi na Manzon Allah (S.A.W) da ke bayani
game da, ba wani abu ne girman kai sai kin
gaskiya"
Zainab ta jinjina kai ganin ya dan tsahirta ya na
duban ta.
"Kin ga duk macen da tare wadannan abubuwa."
Ya ci gaba, "To, babu shakka ta tsira."
"Wannan gaskiya ne Alhaji. To amma ni ban ji ka
tabo bangaren..." Ta yi shiru.
"Bangaren me?" Ya bukata.
"Bangaren su kwalliya, tsafta da kyale-kyale,
kissa don jan hankalin maigida ba, wanda
wannan
ma na san su na daga cikin abin da ke kara
dankon auratayya."
"Ya gyada kai, "Kwarai kuwa Zainab, amma duk
wadannan da ki ka lissafo su na karkashin abu
na uku da na lissafo, wato 'Biyayya', don sai da
ita ne za a yi duk wadannan abubuwa don
faranta wa maigoda rai."
Ita ma ta gyada kai, "Gaskiya ne wannan
maigida."
"Ki na da tambaya cikin wadannan abubuwa
kafin
na je ga shawarar da na ce mi ki za mu yi?" Ta
girgiza kai, "Babu maigida. Na gane su sosai,
kuma da izinin Allah zan dage don ganin na rike
wadannan abubuwa da ya kamata a kira su da
Garkuwar Aure."
Ya yi murmushi, "Haka ne. Abu na gaba da na ke
son na gaya mi ki wanda na ce shawara ne, shi
ne ina so zan sauwake wa Hajiya."
Ta dafe kirji, "Haba Alhaji, yanzu..."
"Saurara!" Ya katse ta, "Idan ban sake ta ba ya ki
ke so na yi da ita bayan ta na karkashin hukuncin
daurin rai da rai? Ki na ganin aurena da ita zai
yiwu ina nan ta na can? Kuma ko ba wannan ki
na tunanin zan iya zama da ita?"
Zainab ta sauke hannunta jiki a sanyaye, babu
yadda za ta iya.
"Ya na ji kin yi shiru?" Alhaji Basiru ya bukata
ganin shirun nata na kokarin tsawaita.
Ta nisa, "Babu koma Alhaji...tausaya ma ka
kawai na ke yi da kuma ita Hajiyar".
Ya yi murmushin karfin hali, "Ni mene ne dalilin
tausaya min din?"
Ta sunkuyar da kanta cikin kunya, "Saboda
bukatarka ta zama da mata biyu."
Ya girgiza kai kana ya yi wani dan guntun
murmushi, "Babu komai amarya, kar ki damu, ke
ma kin wadace ni."
Ta dan harare shi cikin wasa, "Gaskiya kar ka
kuma ce min amarya."
Ya girgiza kai, "Ina! Ai ba zan iya daina wa ba."
Ta gyada kai a takaice, da muryar wasa ta ce,
"Lallai idan ba ka daina ba zan dau mataki."
Ya fashe da dariya, "Ai ba za ki iya ba. Kuma ma
wane mataki za ki dauka?"
"Uhm! Ya wuce na cije ka?"
"Cizo?" Ya bukata, "Ni kuma nawa hakoran fa?
Ba sai na rama ba?"
Ta daga kai su ka hada idanu. Abin da ta gani
cikin idanunsa ya sa ta ce, "Bari na cije ka din ka
rama." Ta yunkura ta kama hannunsa ta sa
hakora.
"Wayyo Allana!" Ya ce da yar daga murya.
Ta sake shi da sauri, ta mike ta yi waje a guje.
Bai tsaya wata-wata ba, ya mike ya bi ta da
gudu.
Dakinta ta nufa ta na dariya. Shi ma dariyar ya
ke Da haka su ka shige dakin.
KARSHE
MUHAMMAD LAWAL BARISTA.
Zaharaddeenn Shomar
Whtapp
Shin Ana Bukatan Blog ko website Kamar wannan kodai kamar Shafin
Duniyan Fasaha, za'a iya samu a kan farashi mai rahusa daga Babban kanfanin
Be With Me Technology Yola, Wayanda suka kware wajen
Website Design da kuma hada Mahajar Waya. Za'a iya tuntubansu
anan ko a wannan layin +2349039016969
Get Professional
Website Design For your business Today
Here. You can also visit our
Tech Blog for more awesome Information.