Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Wednesday, March 22, 2017

bakin lissafi

adsense here BAKIN LISSAFI COMPLETE Awani gari, awata makaranta, awani dare, akasamu gungun wasu matasa sukayi kukan kura suka kutsa kai dakunan kwanan dalibai mata, da misalin karfe 2:30 na dare, dauke da muggan makamai, sukabisu daki daki, suna tattara dukkan abinda yammatan suka mallaka, nadaga kudade, sarkokin gwal, dan kunne da zobban zinare, suka arce dasu a cikin daren, Wan nan salon sata da fashi a makami, ya dade yana ba mutane mamaki acikin makarantar, musamman da safe da aka wayi gari da labarin ta'asar inda aka iske masu gadin hostel din sunsha dauri kamar, huhun goro ashagamu, amma saidai anyi sa'a sosai saboda barayin basu doki daliba ko dayaba, ko yunkurin fyade ga yammatan kudi da sarkoki kawai suka amsa kamar yanda daliban suka bada labari. . Amma anji kishin kishin din cewa wata daliba mai suna, Kubrah ta gane mutum daya daga cikin barayin na daren jiya, wani dan ajinsu ne mai suna Mubarak, wanda ta tabbatar da cewa ta ganeshi, saboda kayan dake jikinsa da su ta ganshi dazu da safe sanda zasu dauki lakcar darasin lissafi, Daidai lokacin da kubra ke labartama wasu kawayenta biyu, cewa ta gane mubarak dan ajinsu acikin barayin jiya, alokacinne wada daliba mai suna jummai, ta zo musu da wani karin labarin kan cewa, ai yanzu kawarta fiddausi take tabbatar mata da cewa itama ta gane mutum daya daga cikin barayin jiyan, yusah'u ne direban gidansu, wanda wata daya baya ya kawota makaranta amotar gidansu, bayan sun dawo hutun karshe zangon karatu na biyu ya sauketa yaja motar ya koma can garinsu. Bayan yammatan sun gama tu'ajjabin wan nan al'amari sai suka rankaya gaba daya suka nufi kofar fita daga rukunin dakunan kwanan daliban mata, inda suka iske wani gungu da yammata suka taru, anan suka iske wat matashiyar budurwace kirista mai suna Ester, an kewayeta tana bada labarin itama fa ta gane mutum daya acikin barayin jiya, mr. Markus ne sabon malamin lissafinsu. Bayan dan gajeren lokaci da yammatan suka dauka suna tu'ajjabin wan nan samame da barayi suka kawo masu adaren jiya. . Tsam wata budurwa matashiya mai suna TANTO, yar asalin kabilar igbo wanda agabanta, aketa nuna alhinin satar da akayi masu ajiya, san nan taji duka lokacin da sauran yammatan suke fadin sunayen wadanda suka gane aciki barayin, ta tsame jikinta daga cikinsu ta sulale ta nufi can cikin makarantar, da niyyar zuwa kai tsaye ga ofishin babban baturen tsaron makarantar wato (chief security) don tsegunta mai sunayen wadanda ake zargi wanda budurwar ta ji sauran yammatan sun ambata. TANTO wata budurwace mai yawan bare bare, da son tsegumi, da son bada labari kamin arigata, don haka cikin sauri take tafiyar, kar wani ya rigata kaima sikuriti labarin, budurwar ta ratse daga kan titin da take tafiya akansa, tabi ta wani rukunin bishiyoyi da sukayi ma wani guri duhu, ta kan wata yar siririyar hanya, wadda daliban suka samar da ita don ragema kansu tsawon tafiya don isa ga dakunan daukar karatu, bayan sun fito daga hostel, wato (short cut) tana tafiya zuciyarta cike da zumudin isa ga inda ta nufa. Ta gitta wata katuwar bishiyar bedi ke nan, wadda tayima wajen kawanyya, sai taji kamar an kira sunanta ta baya, cikin sauri ta juyo, don ganin wake kiranta, don tunda ta shigo dan dajin bata ga kowa ba awajen, musamman da sanyin safiya irin wan nan bakasafai dalibai kan zauna awajen ba, sai can rana ta take tukunna, atsaye taganshi ya jin gina da daya daga cikin bishiyoyin, yana mata murmushi, tabbas indai ba gizo idonta yake ba, malam Marcus ta gani, malaminsu na lissafi, wanda taji kawarta Ester tace ta gane shi acikin barayin daren jiya. Nan take taji gaban ta ya fadi, ya kariko har inda take tsaye, yana kallonta yana murmushi, yace cikin dariya, '' TANTO ina kike nufin zuwa ne haka da sanyin safiya,?'' . cikin alamun tsoro budurwar ta gaza hada ido dashi tace ''zanje lakca ne,'' mr marcus yayi dariya har sauti ya fita, yace bayan ya hade rai, '' a a yammata, zaki je dai ofishin chief sikuiriti, kai rahoton wadanda suka shiga dakin kwananku jiya da daddare suka amshi kudade da gwalgwalai, domin yau asabar nasan ba lakca'' Cikin matsanan cin razani, budurwar Tanto, ta dago kai ba shiri suka hada ido da malamin lissafin nasu, yanzu tabbas fuskarsa adaure take, don haka tasan ba wasa, dama can tasan sa, shi shiri duk in ba na lissafa kudi bane baya a ganin fara'arsa, don yasha nuna masu haka in yana koya masu lissafi a aji, idan yazo wajen lissafa jimillar wasu kudi yaji yawansu har yayi yawa, sai aga kawai yana dariya, yana cewa inama ina tafiya in tsinci wwadan nan kudi. Amma abinda yafi daure ma budurwar kai shine, babu wanda yasan lokacin da ta silalo acikin kawayenta, daga hostel din mata, kuma bata gayama kowa cewa zataje, kai rahoto ofishin security ba, amma taya malam marcus ya samu wan nan labari? Waya gayamai inda zata je? Cikin razani budurwar tanto taja baya, tana dafe da kirjinta, tace tana rawar murya, ''malam way...ya....gaya ma inda zani''? Mr marcus, ya sake daure fuska, yace ''Bansani ba,'' san nan ya sake matsowa inda take, sai ayanzu, Tanto ta lura da kyau , hannunsa na hagu yana rike da wata karamar bindiga ne kirar pistone, ya danyi kasa da muryarsa san nan yace, . ''Bake kadai ba, ina sane da cewa Kubra ta gane mubarak dan ajinsu adaren jiya, san nan fiddausi, ta gane yusha'u diren gidansu, ni kuma ester ce tayi sa'ar ganeni, don haka afarke muke shirin mu,'' adaidai lokacin ne, ya daga hannunsa mai rike da binga, ya saita daidai ruwan cikin budurwar, yar inyamurar ta sake rikicewa, dama gata gwanar tsoro, tace tana kokarin fara kuka, '' don Allah malam karka kasheni, wallahi tallahi, na rantse da kwaran kwatsa bazan gayama kowa ba,'' da alama yar budurwar ta gama rikicewa, mr marcus ya zazzaro mata idanu, yace cikin murya mai dan karamin sauti, '' maza ki gayamin mutum nawa suka san wan nan labarin banda kubrah, da fiddausi, da Ester dake?'' Cikin rawar murya, Tanto tace, '' wallahi bamu da yawa bamu wuce mu goma sha uku ba,'' amma na baro suna ci gaba da gayama wasu'' mr marcus ya gyara tsayuwar bindigarsa, adaidai cikin matsoraciyar inyamurar, yace ''maza, da sauri ki koma ki kiramin yammatan uku, ki samesu daya bayan daya, kar wata tasan da wan nan gayyatar wanda ba suba, in bahaka ba kuwa, kinga wan nan bindigar,'' ya dannata acikinta, saida kan bindigar ya taba ruwan cikinta, san nan yaci gaba da cewa, sai ta fasa tumbinki ta ragargara kashin bayanki, in kika kuskure baki dawo tare da su ba, zan biyoki har hostel din, adaren yau na kasheki'' Tanto ta sake tsurewa, tace ''To malam'' cikin rawar jiki, ta bi siririyar hanyar data shigo da ita rukunin itatuwan ta koma inda ta fito, bindigar mr marcus na mata rakiya daga nesa. Tunda matsoraciyar budurwar nan Tanto, ta juya ta nufi can rukunin dakunan kwanansu, don cika ummarnin malaminsu na lissafi mr Marcus, ta kira sauran yammatan da suka fara fallasa asirin wadanda suka afka dakunan kwanan su acikin daren jiya suka tattara komai nasu suka arce dashi. Da sauri matsoraciyar inyamurar take tafiya, bata iya waigawa saboda tasan saitin bakin bindigar da mr marcus ya saitata tashi shike mata rakiya har yanzu, . kuma aranta tana gargadar kanta da cewa tabbas mr marcus zai iya aikata danyen aikin daya ambata akanta, muddun ta gaza kiran yammatan zai biyota har dakin kwananta ya karya mata kashin baya da harsashin bindigarsa, don kallo daya zakaimai ka tabbatar da fuskarsa ta dade tana lissafa kudi atakarda, wanda zuciyarsa ayanzu take ta fafutikar son taga ta mallaki kudin da yaya kwashe shekaru masu yawa, yana lissafasu afararen takardu, don haka komai yana iya yi akansu. Tun daga nesa Tanto ta hangi kawarta Ester tana tsaye da wasu yammata biyu abakin babbar kofar shiga gine ginen dakunan kwanan yammatan, da'alama labarin take gayamusu, da sauri ta isa gareta, ta jata gefe guda tana rawar baki tace, ''ke ester asiri ya tonu, malam Marcus nacan (forest garden) yace na kiraki, kuma wallahi naganshi da idona bindigace ahannunsa, yayi barazanar kashemu gabaki dayanmu, muddun muka kara yayata wan nan maganar, yace muyi sauri yana jiranmu,'' Budurwar yan asalin kabilar yaroba, ester ta zazzaro ido tana sauraron kawarta tanto, dama tafi tanto tsoro, domin ita duk wani abu da ka iya sawa ayi labarin mutuwa, ester bata kaunarsa ko kadan, ance gidansu idan akayi mutuwa takanyi wata daya cur bata gidan ko leko kofar gidanba tayi, don haka wan nan mummunan labari da tanto ta kawo mata, yasa nan take taji cikinta ya duri ruwa, domin kuwa ta san akalla ta labartama mutum sama da shida wan nan zance, tace cikin firgici, ''yanzu to ya zamuyi'' Tanto tadan gyara tsayuwarta, fuskarta cike da zufa, dukda iskar safiyar da take kadawa, tace tana kallon estar ''Ai yace harda su Kubra da fiddausi na kira su, kuma nasan su zai wahala suje, in sukaji shi ke kira, domin dama basu cika shiri dashi ba, musamman fiddausi, don haka zamuce malam Kabir ke kira, ya samu labarin abinda ya faru'' Atare yammatan su hudu suka rankaya suka nufi cikin makarantar don amsa kiran malam marcus, kamar yanda yammata biyu suka san shike kiransu, sauran yammatan kuma kubra da fiddausi, . zasu wajen malam kabir ne, (Dean students Affairs) don kara jaddadamai abinda ya faru dasu adakin kwanasu adaren jiya, cikin sauri yammatan hudu suka ratsa ta (short cut) dinsu, yar siririyar hanyar da zata sadasu ta can cikin gine ginen makarantar daga dakunan kwanansu, sun isa tsakiyar rukunin itatuwar da sukayima hanyar duhuwa ne, daidai (Forest garden) sai sukaji kamar daga sama ance '' Barkanku da zuwa yammata,'' cikin firgici da rashin tsammani yammata uku suka waigo inda sukejin muryar, amma tanto wadda tasan da zaman mai muryar awajen wan nan baisa ta razana ba. Mr marcus ne, ya silalo ta bayan wata bishiya, ya nufo yammatan fuskarsa adaure, saida yazo gab da su san nan suma suka lura hannunsa na hagu, yana rike da karamar bindiga, nan take gabaki dayansu suka tsure, yadan yi masu murmushin yake, san nan yace yana dubansu daya bayan daya, ''sannuku yammata gwanayen kamu,'' nan take kubrah da fiddausi suka fahimci inda lissafin malamin lissafin ya nufa, yaci gaba da magana yana kallonsu, ''Tanto kin gama naki aikin da kika tattaromin masu idon gane bakinsu na jiya'' mr marcus ya hada hannuwansu biyu yayi tafi da karfi, lokaci daya kamar daga sama, sai ga mubarak dan ajinsu, Kubra ya fito shima daga bayan wata bishiyar tunfafiya dake awajen yana ma yammatan murmushi, yusha'u direban gidasu fiddausi, shima ya biyu bayansa, yana sanye da wasu kanan kayan daya shiga dakin kwanna yammatan dasu, daga bayansu karin wata tawagar samarin ne matasa wadanda dasu aka afka dakin kwanan yammatan ajiya. bayan sunyima yammatan kuri, sun kewayesu, sai mr marcus ya kallesu alokaci daya, ya daure fuska, ya daka musu tsawa, yace cikin kakkausar murya, bandaku dawa dawa kuma suka san wan nan labarin matsa ku gayamin insa akawomin su nan, don na yanke maku hukunci tare'' 5 minutes ago · Sent from free.facebook.com Ismail Sani ............................... Yammatan suka kalli malamin lissafin nasu, mr marcus alokaci daya, suna zare idanu, cikin alamun tsoro da firgici, da fadawa wan nan tarkon mamuguncin malamin. Dama tuni sunsan malamin azzalumine, bashi da tausayi kokadan, don yasha kada dalibai ba gaira ba dalili, a darasin lissafin daya ke koya musu, san nan aduk lokacin daya koya masu wata fomula ta lissafi yaga sun gaza ganeta, sai yayi ta musu dariyar mugunta, yana fadin, (its my time) wan nan yasa dayawa daliban makarantar suka tsani malamin, musamman ma fiddausi, da kawarta kubrah. Tonto da Ester sune sukafi sauran yammatan tsorata, da irin barazanar da marcu yake musu, don dama kabilu ance sunfi hausawa tsoro, tun bayan yakin basasa da akayi anigeria, akayi musu kaca-kaca, suka fada razani da tsoro matuka, yar budurwa Ester da take gaf da fara gudawa atsaye ta kalli mr marcus da ya saitata da bakin bindigarsa, idonta cike da hawaye tace '' wallahi malam wadanda na gaya mawa bazasufi mutum tara ba, ciki harda baba na dake can garinmu da... . '' Ester ta tsuke bakinta ta gaza cigaba da bada bayanin ganin idon marcus na sauyawa daga ja zuwa wani kore kore, ranshi abace, ya sake matso kusa da ita, yace cikin siririyar murya mai alamun zafi, ''banda babanki wa kuma kika gayamawa agidanku? Kuma saikin gayamin abinda kika gayamusu, kona tarwatsa katon kan nan naki,'' ya dora karamar bindigar adaidai goshin matsoraciyar budurwar. Ester ta saki fitsari atsaye, cikin rawar murya, tace ''wallahi bangaya musu komai ba, cewa kawai nayi kaine kayi mana sata adaren jiya, yace zaizo makarantar don adauki mataki, bandashi ban gayama kowaba,'' mr marcus ya dan saki fuska, don yasan barazanarsa ta yi tasiri akan budurwar, ya juya da sauri akan sauran yammatan, kubra dake gefensa na dama yafara tuhuma, ke kumafa dawa dawa kika shelantama wan nan labarin,? Kubrah tadan ja baya atsorace ganin mamuguncin malamin yana matsota, dauke da bindigarsa ahannu, tace nata lura da motsin hannunsa mai bindigar ''mutum uku kawai nagayamawa,'' ''banda sufa'' marcus ya tambaya yana kallonta da jajayen idanunsa, ''wa kika gayamawa agida, don in nagano kema kingayama wani agidanku, baki fadamin ba yanzu, saina harbi wan nan dogon hancin naki, harsashina ya ketashi hudu, ya fada cikin kanki yayi raga- raga dashi,, . ''wallahi bangayama kowa ba bandasu'' Mr marcus ya kalli Fiddausi wadda suka dade suna tsama da ita, dama ya dade yana fatan budurwar ta fado komarsa, don ya taba nemanta, da lalata tayimai mummunan wulakanci san nan takai kararsa ga hukumar makarantar, aka dakatar dashi na wani lokaci, tundaga wan nan lokacin ya samata maki, don haka yayi mata dan murmushin dake alamta muguntarsa afili, yace bayan yadan daure, ''ke kumafa yamamta, maza ki gayamin wanda kika gayamawa, yau baramar wasa bane, zan iya karya wan nan siririn wuyan naki, duk kyawun nan naki bandamu ba, indai akan kudine, dawa dawa kifa kwarzantamawa wan nan labarin, maza sauri muke muje bincike karo na gaba'' Fiddausi ta dafe kirjinta, ganin lallai mr marcus da gaske yake wan nan furucin nashi tace tana rawar murya ''mutum uku nima nagayamawa, sukenan, wallahi, bangayama kowaba baya gasu,'' Marcus ya gyada kai alamar gamsuwa, yace ''dakyau, da kukayi dubara kuka takaita labarin, yanzu kuyi maza ku tahomin nan tare da sauran yammatan, da duk suka san wan nan labarin zan hadaku da yarana mutum uku, wadanda baku iya ganesu ba, zasu biku amatsayin security, don fara binciken badakalar, don haka sai ku fada musu, su basu hadinkan tahowa dasu nan yanzu, in bahaka ba, abinda zai biyo baya yafi wan nan muni'' yadan sarara yana duban yammatan da tuni sun gama tsorata, san nan ya dubi budurwa Ester wadda tuni ta gama jike dan gajeren siket dinta, yace kece kikayi gaggawar shaidama babanki wan nan labarinko, yanzu kinjamai, shigowa tarkona, yanzu zanje na taho dashi nan, shima don amsar irin hukuncina'' . Yammatan hudu suka juya atsorace, wasu matasa guda uku, . daga cikin tawagar Mr marcus, suka rufa masu, baya, suna sanye da kananan kaya, ko wannensu ya toke sun sanya biruka agaban aljihun rigunansu, biyu sanye da fafaren tabarau na fuska, suna tafe suna dan taba hira da yammatan, kai kace wasu jami'an leken asirine daga hukumar yansandan ciki, nan ko sune barayim da sukayi kitse acikin dakin yammatan adaren jiya suka tattare komai nasu suka arce dashi. Mr marcus da sauran yaransa, suka boye acikin duhuwar itatuwan dake kewaye da (forest garden) suna jiran dawowar yaransa da tawagar yan matan, san nan yayi maza ya sauya musu guri don samun damar gudanar da bincikensa akansu mai tsafta, da niyyar shima zai bazama garinsu, matashoyar budurwa yar kabilar yaroba Easter don gayyato babanta wanda yanzu haka yasan da labarin su marcus ne suka shiga dakin kwanan yammatan. . Tattaro yammatan baiba yaran mr marcus wahalaba sosai, saboda suna isa rukunin dakunan kwanan yammatan, suka isa harabar gine ginen, nan da nan yamatan suka shiga daya bayan daya suka kira yammatan, sai dai anyi rashin sa'a wata budurwa mai suna SUWAIBA, dake kauyen Kaimon kaura, wadda kubra taba labarin al'amarin ta buga sammako tun bayan fitar su kubran zuwa amsa kiran mr marcus, ta nufi gida can kauyensu. Cikin sauri kubra tabi bayanta har bakin karamin get din fita makarantar, amma saidai kash tun kamin ta karika bakin get din ta hangi motar bus ta tashi daga bakin get din kuma tabbas matashiyar budurwar suwaiba ta dauka, da alamama ta dade bata samu mota ba kenan. Kubra ta dawo jiki ba karfi, don tasan muguntar mr marcus, zai iya dora mata laifin, amma saidai yaran marcus da suke tare da ita sun shaida tafiyar budurwar, suka tattaro sauran yammatan suka nufi inda mr marcus yake tare da sauran yaransa. Mr marcus dake makale abayan wata bishiya, ya dan dago agogon dake hannunsa inda idonsa suka ci karo da karfe 10 daidai na safe, nan take yayi saurin kewayowa inda sauran yaransa suke yace cikin daga murya, dole muyi sauri mu bar wajen nan, don nasan lokaci ya fara ja, mutane zasu fara yawa acikin makarantar nan domma yau week end, Yusha'u maza ka kawo mana mota mubar wajen nan. . Lokacin da tawagar yammatan suka kariko gurin wata doguwar mota suka iske mai kirar motar safa, sauran samarin na ciki, batare da bata lokaciba, yaran mr ,marcus dake tare da tawagar suka basu ummarnin kutsakai cikin motar, yammatan suka shiga batare da gaddamaba, saboda abinda idanunsu ke kallo rike ahannun sauran matasan dake cikin motar. Marcus dake gaba yayi murmushin mugunta, san nan yace ''yusha'u ja mota muje,'' daya daga cikin yaran marcus da sukaje tahowa da yammata, yace yana kallon marcus, oga akwai wata yarinya daya da bamu samu ba, tayi sammakon tafiya gida, kuma kubra ta gayamata komai game da aikin. Marcus ya juyo fuskarsa adaure, yace ''wacce yarinyace kuma inane kauyensu, ? Dole ayi sauri adawo da ita kamin takai gida don kar wani yaji labarin nan daga gareta.'Tunda Yusha'u direban gidan su Fiddausi, ya sharari motar asukwane, atsiyace ya fita makarantar don gudun cin karo da wani daga cikin jami'an makarantar yaganasu. Saida suka hau kan babban tintin dayabi ta gaban makarantar san nan yusha'u ya dubi mr Marcus dake zaune daga gefensa, yace ''oga ina muka nufa daga nan?'' Mr marcus cikin mazurai ya kalli direban dake ta caccakama motar wuta, yace ''tsohon gidan gonar Alhaji Manga zaka kaimu, inada masaukin da aan ajiye dukkan yammatan nan acan, san nan mu fita farautar saura. Dukkan yamatan hankulansu atashe suke, tabbas sun san yau sun fado tarkon azzalumin malamin lissafinsu, mr Marcus, kowacce zuciyarta cike da damuwa da sake saken halin da zasu iya shiga muddun mamuguncin mutumin yakaisu inda yake nufi, bama kamar yammatan kabilun nan Easter da Tanto, wadanda sunfi tsurewa musamman ganin yanda yaran marcus suka tasasu da bakin bindiga, kusan sau bakwai kenan Ester nacewa atsaya zatayi fitsari acikin minti ashirin, saboda tsabar firgita. Bayan tafiyar minti talatin tawagar mr Marcus ta sulala,cikin mataccen gidan gonan wanda ya dade da mutuwa saboda yanda aka kyaleshi ba'a anfani acikinsa dakomai ahalin yanzu, yazama mafakar yan ta adda irinsu marcus, sukayi fakin adaidai kofar shiga wani tsohon gini, wanda da'alama rufinsa duk yafara zazzarewa saboda dadewa da'akayi ba'a shigeshi ba. Mr Marcus ya fara fitowa daga cikin motar, ya nufi kofar shiga ginin gidan gonar, san nan yasa wani karamin mabudi ya bude kofofin san nan yayi ummarni da ashigo da dukkan yammatan, bayan shigar yammatan dakin sunyi mamakin yanda sukaga dakin atsaftace, an shinfida kafet tare da jerin wasu kujerun alfarma, kai kace gidan wani attajiri ne, yammatan sun shiga cikin kokonton cewa lallai marcus ya shiryama kawo nan gidan dama can tuni, daganan suka fara fargabar Allah yasa kada suyi yunkurin lalata masu rayuwa. . Cikin sauri mr marcus batare daya waiwayi inda yammatan suke ba, yacema yaransa, '' Mutum uku zasu tsaya nan suyi gadin yammatan nan, mubarak dakai yusha'u zakuyi maza yanzu kubi sawun Suwaiba kamin takai kauyensu ku tabbata kun dawo da ita nan, zaku iya tafiya da wan nan motar, ni kuma zan tafi garinsu Easter zan taho da tsohonta, nan da karfe 2:00 daidai na rana mu hadu anan tare da bakin nanmu, ku kuma ku kula da yammatan nan duk wanda nakama da yunkurin fyade ga wata acikinsu, sai na halakashi, mu kudi muke so da rufin asiri.'' Alokaci daya dukkanssu suka fice daga dakin atare, marcus ya nufi garin su Ester , mubarak kuma da Abokinsa Yusha'u suka nufi kauyen KAIMON KAURA don dawo da suwai ba kamin ta gana da iyayenta. Tunda Suwaiba ta shiga tsohuwar motar kirar Bus, daga bakin kofar makarantarsu, zuciyarta cike da zullumin halin da masoyinta zai kasance tun adaren jiya, shiyasa adaidai wan nan lokaci dukda gudun damai tsohuwar motar yake shekawa, akan kwaltar, suwaiba ji take kamar turasu akeyi da hannu, cikin kagara tadan gyara zaman ta san nan tace cikin daga murya, ''direba don Allah sauri nake kadan kara daga kafa'' Cikin fushi matashin direban yajuyo yana kallonta, wanda yasan ya gama kure malejin gudun tsohuwar bus din, amma sai gashi wata tana raina gudun motar, wanda shi yafi kowa zalamar son gudun, saboda tunjiya aka gayamai yayo sammako TASHAR TABARE, wani karamin kauye daka wuce hanyar shiga KAIMON KAURA, inda zai yi lodin wasu kwandunan tumatiri, dukda haka direban ya hadiye fushinsa, yakara caccakar motar kukan ta ya sauya, yaci gaba da dibar hanya. Suwaiba tayi shuru, kaikace an aiko mata da labarin mutuwa ne agida ake nemanta da gaggawa, acan cikin zuciyarta ba abinda take tunani yake kaikomo kamar tunanin saurayinta, SAMANJA, Wanda take mutuwar sonsa, shima yake mutuwar sonta, adaidai wan nan lokaci tasan shima hankalinsa na kanta, domin adaren jiya tun misalin karfe shabiyu da rabi nadare, suke free call dashi, suna dandasa labarin soyayya, kwatsam mazajen dare suka fado dakin, tana kokarin gayama samanja wata kalmar soyayya da yake bala'in jin dadinta, wuf cikin barayin wani ya fige wayar ya dadata da kasa, nan take ta tarwatse. . Don haka suwaiba tasan tabbas in samanja yayi wunin yau ban sameta awayaba, babu abinda zai hanashi niko gari ya biyota makaranta, zuwansa makaranta kuwa zai iya zama mata hadari, saboda muddum yaji labarin abinda ya faru, babu abinda zai hanashi daukar mata fansa, acikin mummunan mataki, domin sarai suwaiba tasan halin saurayin nata, Firgigit Suwaiba ta dawo daga duniyar dogon tunaninta, alokacinda taji tsohuwar motar bus din takusa hantsalawa dasu, tana kujerar baya saura kadan kanta ya bugu da kujerar dake gabanta, ashe tsabar take burkine, da direban yayi adaidai hanyar shiga wani kauye, inda ya hangi wani fasinja na jiran mota, dakyar direban ya take burkin saboda gudun dayake shekawa yayi yawa, dukkusan fasinjojin motar babu wanda baiyi ma matashin direban korafi ba, ganin akan fasinjan naira ashirin zai halaka su, don dakyar yasha kan motar tana wani irin kara, suwaiba dai batace komai ba, [8:59PM, 8/22/2016] Usman Auwalu Zango: BAKIN LISSAFI 7 .´ Don ta lura akokarin cika burinta na sauri direban yayi masu ganganci da rayuwa. Bayan yadauki fasinjan ahankali yacigaba da canccakama motar giyoyi, ta sake lulawa akan titin, amma anja kunnansa akan lallai ya rage gudu da motar saboda hanyar bata dakyau sosai, san nan inyazo tsaayawa karya kassarasu abanza Ya rinka sassauta gudu tun daga nesa. Bayan tafiya ta kara lulawa, nan danan Suwaiba ta sake gayyato daddadan tunanin da yake yanke mata bakin cikinta, wato tunanin saurayinta samanja, dukda awan nan karon tunanin yafado mata ne arai daidai inda bai cika mata dadi sosai ba, wato duk sanda suwaiba zata rinka tuna irin halayen saurayin nata SAMANJA, takan dan shiga damuwa,amma saboda irin son da take masa yakansa ta ga halayensa kamar basu da aibu sosai, amma amaganar gaskiya, SAMANJA, rikakken dan dabane, wanda ya dade da samun tikitin shiga duniyar rigima da data zaune tsaye atsawon lokaci, gashi baida hakuri, tun yana matashinsa shida wasu bata garin abokansa, suka addabi kauyen kaimon kaura da sace sace, tun a wata shekara da aka taba kamasu sunje rigar wasu fulani suka sace masu wasu manyan bajiman shanu, tundaga nan akakai su gidan maza shekaru biyar, ana zaton da Samanja ya dao zai natsu ya zama mutumin kirki, amma ina sai akaga akasin haka, ashe acan samanja ya hadu da manyan yan fashi da makami, ya shiga kungiyarsu, shekarunsa uku a legas suna gudanar da sana'ar fashi da makami, tundaga san nan aka sallama ma, samanja. . Amma babban abinda yafi ba mutane mamaki da babban dan ta addan shine, duk inda yaje tabargazarsa, sai ya dawo gida yaga sahibansa Suwaiba, an dade ana shan mamakin irin wan nan matsanancin soyayya da samanja kema Suwaiba, asanadiyyarta nema ayanzu yadan rage fita yaje ya dade, saboda baya son nisa da ita, Ayanzu abinda yafi yawo azuciyar suwaiba game da tunanin hatsabibin saurayin nata, shine awasu shekaru baya ya taba sare hannun wani saurayi don kawai yace yana sonta, san nan ya sari wani akai da adda, yayi mai mummunan rauni, shima don kawai yace yana son suwaiba, wan nan yasa dayawan samarin karkarar suka kiyayi kusantar budurwar don tabbas samanja yasha alwashin, kisa akan duk wanda hukuncinsa ya hau na sabama dokarsa na nesantar masoyiyar tasa. Wani kwazazzabo da motar da tsohuwar motar tafada ita ta sake dawo da kowa cikin hannayacinsa, da wasu mata biyu dake kusa da suwaiba wadanda suke sharar bacci suka farka firgigi, wan nan yasa suwaiba ta hango babban sambol din dake nuna hanyar shiga kauyen su na Kaimon kaura, tun kamin ta kainga sauka, ta hangi masoyinta Samanja, abakin titin, da'alama mota yake jira, kusa da wata rumfar yayi da wasu masa sukayi suna sana'ar bunburutu. Suwaiba tacema direbanA inkaje kaimon kaura akwai mai sauka, direban ya girgiza kai alamar yaji, daganan ya fara kokarin take burkin motar wadda take ta sheka gudu, dakyar yasamu ya faka bayan yayi ma hanyar shiga kauyen nisa, wan nan yasa saida suwaiba ta dako akasa ta dawo daidai kwanar shiga kauyen nasu, san nan ta karika ga sahibin nata, wanda shima tun daga nesa ya hangota ya runtumo asukwane, tun kamin sukaiga haduwa, sukaji karar taka burki adaidai gabansu, wata doguwar mota fara kirar ta yan makaranta, ta sha gabansu, cikin sauri kofofin motar ta bude wasu samari biyu suka fito MUBARAK ne da YUSHA'U, yaran malam Marcus. Da fitowar samarin biyu daga motar, mubarak da abokin ta'addancinsa Yusha'u direban gidan su fiddausi, kai tsaye wajen yar budurwar suka nufa Suwaibam wadda ke kokarin karikawa ga Sahibinta Samanja dan daba, dake daga bayansu. Sam samarin biyu, basu lura da matashin dake daga bayansu ba, kai tasaye yar budurwar suka nufa suna murmushi, alokaci daya Suwaiba taja ta tsaya ganin matasan na nufota, saida suka kara matsowa san nan tayi sa'ar gane mubarak tabbas itama ajinsu daya dashi, shine wanda Kubra ta basu labari yana cikin barayin jiya da daddare, nan take Suwaiba taji gabanta ya fadi. SAMANJA dake daga can baya yana kallon samarin biyu sun shiga tsakaninsa da budurwar tasa, cikin sauri ya jefar da wata tsohuwar jakar dake hannunsa, wadda ya dade yana zuwa yawon farauta da ita, amma duk da haka idan wata mahimmiyar tafiya ta kamashi da ita yake tafiye tafiyensa, ya taho da gudu, musamman yanda yaga daya daga cikin matasan ya cakumi hannun sahibar tasa Suwaiba suna kokarin jefata a mota. Mubarak ya zaje kofar motar da sauri ya jefa matashiyar budurwar aciki, san nan ya fada ciki shima tunu yusha'u ya tada motar yana kokarin komawa kan kwalta, adaidai lokacin Samanja ya kariko jikin motar yanajin sautin muryar Sahibarsa Suwaiba tana kwalla ihu da kiran sunansa. Amma ina tuni motar ta sheka da gudu akan titin, tare da fizgar hannun Samanja da ya rike jikin hannun murfin kofar ta waje, nan ya fadi agefen kwaltar saboda karfin fizgar da direban yayi ma motar, da sauri wasu samari dake can cikin wata runfar yayi suna sayarda man fetur na bunburutu, dake gefen titin suka yo kan samanja dake kokarin tashi, suna tambayarsa abinda ke faruwa. Dakyar samanja ke nuna masu motar, saboda zuciya da takaicin anzo har gida ancishi da yaki, abinda ba'ataba yimaiba kenan arayuwa, lallai dole sai yabi sahun mutanen nan ya dawo da sahibarsa, koda dukkan garin zasu kare kuwa, ace budurwar dayafi kauna aduniya, anzo agabansa an saceta, lallai ba'a nemi zaman lafiya ba, nan danan samanja ya tarbi wata mota dake kokarin wucewa ta kan titin, ya fada ciki batare da fadin ina ya dosa ba, yace ma direban cikin damuwa, . don Allah malam waccan motar nakeson kabi, wallahi sahibata aka sace yanzun nan agabana, barayin mutanene, dayawa fasinjojin motar sun dauka Samanja wasa yake, don wasu ma dariya suke, saboda kallon mashayi da suke yi masa, da siffar yan daba marasa imani. Amma daga karshe sun fahimci da gaske yake, saboda yanda yake karajin damuwa, ta nuna bayan motar, wan nan yasa direban kara sakin motar akan titin ko sa samu su isa ga doguwar motar dake can gabansu, dukda suma wadancan motar masifar gudu suke, motar gudu take shakawa kamar zasu lahira, don su samu su taddo da farar doguwar motar da suke hange can agabansu wadda alokuta bayan lokuta takan bace musu, saboda hawa ko kwana da gangara, sai sun fita san nan suke iya kara hangenta. Suna cikin masifar gudun ne an kusa shiga gari sai suka hangi motar ta dauke kwanar shiga wani kauye ta cikin wata hanyar burji, nan danan Samanja yace dakaje can ka sauke ni, tunkamin sukai samanj ya ciro kudin motar mutumin ya bashi yana godiya, daya taimakamai ya biyo motar da gudu. Daga bakin hanyar zuwa gidan gonar da Mr marcus ya boye yammatan bai fi kilomita daya ba, acikin wani daji ne, inda wasu tsaunuka suka kewaye wajen, don haka da gudu mubarak da abokinsa Yusha'u shuka fada gidan gonar suka nufi dakin da yammatan suke, tare da budurwa Suwaiba ta Samanja, suka iske Mr Marcus da sauran yaransa, suna tsaye suna jiran dawowarsu. Mr Marcus ya tarbesu cikin farinciki ganin sun dawo tare da suwaiba tana ta faman rusa kuka, saida marcus yayi barazanar tarwatsa kanta da harsashi san nan ya samu tayi shuru, ya kalli su mubarak dake tsaye daga baya, yace dakyau aikinku yayi kyau, don haka tare daku zamuje yanzu mu taho tare da Mahaifin Ester, . da nayi niyyar tafiya nikadaine amma sai bayan kun tafi nayanke shawarar na jira ku dawo mu tafi tare saboda irin wadan nan kabilun namu nasansu, suna ajiye bindiga don bacin rana, kada ya mamayeni, amma yanzu inada yakinin tafiya dashi acikin ruwan sanyi. Marcus yasan sarara yana kallon yammatan yaci gaba da cewa '' amma kamin mu tafi yanada kyau muyima yammatan nan karin haske, don nasan har yanzu wasu acikinsu musamman fiddausi suna mamakin taya Yusha'u dayake direban gidansu yazo nan makaranta, alhali shi badalibi bane, san nan taya muka hadu dukkansu dashi, har muka yanke shawarar afkawa dakinsu don farautar su adaren jiya'' Marcus yadanyi murmushi san nan yace, ''yammata ku kwantar da hankalinku, asannu zaku san nan wan nan dalilin, Yusha'u shine wanda ya fara zuwa da wan nan labarin nan makarantar, saboda yana aikin tuko agidansu fiddausi tsawon shekaru yana luda da irin yanda iyayenta ke siya mata sarkoki da kayan alatu na mata masu tarin yawa, ni kuma nasan yusha'u tsawon shekaru lokacin da ina sana'ar tukin mota daga gari zuwa gari [7:48PM, 8/25/2016] Usman Auwalu Zango: BAKIN LISSAFI 9 . yataba riyin yaron mota, don awajena ya kiyi tuki, daga baya muka rabu dashi, bayan na koma makaranta, shi kuma ya sami tuki agidansu fiddausi, babanta babban hamshakin attajirine,'' Marcus ya sake murmushi yace na yammacin shekaranjiya yusha'u yazomin da labarin cewa ya dawo dafiddausi makaranta bayan hutun daka kwashe, tabbas ta dawo da kayan gwala gwwalai masu tsadar gaske, wanda shikadai ya isa babban jari, wan nan yasa na gayyato yarana mubarak da wadan nan, wadanda dama su mun dade muna sana'ar boye dasu, fiddausi kadai muka sa atsarin wadda zamu lalube, amma ganin munshugo gine ginen dakunanku sai muka sauya shawarar, samun ribar kafa, muka biku daya bayan daya, sai gashi kuwa mun samu ribar fita mai yawa'' Mr Marcus na zuwa nan azancensa, ya juya yace '' wan nan kenan, don haka zamuje mudawo duk wadda tay yunkurin guduwa ga yara nan uku, biyu awaje daya zai tsaya nan tare daku, zasuharbe duk mai karar kwana, na taraku ne don bana son barain ya fita, zan tattara duk wanda yasan labarin san nan na hukuntaku agare nan da zuwa la'asar kowa yasan makomarsa acikin aikina, karku damu,'' marcus yaci gaba da dariya yana tafiya. Mubarak da Yusha'u suka take mai baya, suka dauki motar suka fice da gudu daga gidan gonar suka nufi garinsu Easter don taho da mahaifinta. Samanja dake rakube abayan wata bishiyar dorawa ya hangi fitowar motar daga gidan gonan, kuma tabbas ya shida matasan da suka sato sahibarsa ne aciki.. . Bayan bacewar doguwar motar safar, wadda mr marcus da yaransa biyu Mubarak da Yusha'u ke ciki, da sauri SAMANJA dake boye abayan wata katuwa bishiyar dorawa, ya fito fili daga kefen wat siririyar hanya wadda zata sadaka da gidan gonan da suka fito. Bayan Samanja ya hangi motar tasha kwana alokacin da ta hau kan kwaltar ta sheka asukwane, nan danan ya gyara takalmin dake kafarsa, wani tsohuwar kwabane sawu ciki wanda ya ciwoshi awajen caca a wasu shekaru can da suka wuce, yawanci da takal,in s,anja kanci bagu in ana wani biki akauyen ko zashi wata mahimmiyar unguwa. Cikin hanzari ya nufi gidan gonar, yana tafiya yana nazartar yanda wajen yake, tabbas samanja yasan babban aikine agabansa, na kokarin kubutar da sahibarsa daga hannun wadan nan miyagun kamar yanda yake fada aransa, don abinda zuciyarsa take shaidamai game da mutanen shine tabbas yan yankar kaine, don haka yanada yakinin saida su mutu tare da Gimbiyarsa Suwaiba, amma bazai iya tafiya ya barta ba, don haka asannu ahankali zuciyarsa tafara yimain doguwar tariya, wani zamani can baya, sanda ya taba satar toron agwagwar wani makocinsu Malam Audu badaskare, yatafi kasuwar gangaren masaka, zai saida sukayi kicibis da malam Audu shima yaje cin kasuwa, lokaci daya malam Audu ya ya gane toron agwagwarsa, yayima Samanja ihu atare tare acikin kasuwa, dakyar samanja yasha, bayan yasha duka da itatuwa, tunda ga wan nan lokaci samanja bai ko koma kauyensu Kaimon Kauraba ya je tasha ya lalubi motar legas ya nufi gudu. Babu abinda ya sauya bayan isar Samanja legas, acan ya hadu da kungiyar wasu barayi yan fashi da makami, wadanda daga karshe suka tashi daga legas suka koma jahar Anambara, acan ne suka dinga cin karensu ba babbaka. Ayanzu haka da Samanja ke tunkarar gidan gonar da yake tunanin yan yankar kaine suka sacemai Habibinsa, ba abinda yake tuwana sai wata rana da suka taba shiga gidan wani Inyamuri a jahar Anambara da niyyar yimai fashi da makami, sun isa gidan kusan karfe 3 nadare, tare da manyan makami, ashe mutumin shine babban jagora awata kungiyar asiri ta matsafa dake wani kauye na OTELLUA dake jahar ta anambara, su shida suka sami nasarar shiga gidan ogan, amma Samanja kadai ya tsira da rayuwarsa, sauran duka wani tsafi da iyamurin yayi ya cinyesu nan take suka mutu, shima SAMANJA ya samu kariyar wata layar zanane da asirin shashatau, da wani abokinsa dan Fulani ya taba bashi, da kyar ya gano hanyar kauyensu daga can Anambaran. . Don haka ayanzu da zuciyar samanja take masa tariyar wan nan rijiya dabaya dayata tsallakewa, zuciyarsa ta dan karaya kadan don tabbas suma wadan nan dayake tunkara baisan irin hatsabibancinsuba, gashi kuma ya baro layar zanarsa gida baizo da komai ba, amma dukda haka yakan samu karfin gwiwa da zarar yatuna Gimbiyarsa fa wadda yafi so da kauna tana cikin gidan nan, don haka sai ya san halin da take ciki koma ya tafi da ita, wan nan yasa ya samu cikakken karfin gwiwa nan take ya kutsa kansa cikin dan karamin gidan gonan, cikin taka tsantsan da lura da motsin dake atashi aciki, Samanja ya taka sannu ahankali cikin sanda tare da boyewa abayan kananan bishiyoyin dake cikin gidan gonar, bayan ya wuce wasu kanan rukunin bishiyoyi can daga nesa ya hangesu wasu matasa ne guda biyu kowannensu rike da bindiga ahannu sunata sintiri agaban kofar shiga wani daki, can kasa kasa Samanja yaji kamar tashin muryar Sahibarsa Suwaiba tana cewa ''Wayyo Allah sahibina Samanja maza kazo ka ceceni, don zasu kasheni alhali banyi masu komai ba. Samanja ya dago kansa sannu ahankali, bayan sun hada ido da matashin katon dake tsaye abayansa yana rike da wata madaidaiciyar bindiga, tabbas samanja yasan sharrin bindiga, domin aduk yawon duniyarsa sunsha arangama da jami'an tsaro, yasha gani yanda ake harbe abokan sana'arsa suna mutuwa har lahira da harsashi kwaya daya tal, don haka yasan sharrin bindiga zuwa daya take ma mutum, wan nan yasa juyowa ahankali tare da mika wuya cikin biyayya ga matashin dake rike da bindigar. Samanja ya tuna a sanda yana tashen kauranci, yataba shan maganin bindiga, saidai yasan maganin tuni ya karye, domin acikin sharadain karyewar maganin ance mai kar ya sake yayi soyayya da kowacce budurwa, don haka tuni yayi fatali da wan nan sharadi ya tsunduma soyayya da Shaibarsa Suwaiba. Gabjejen matashin ya tasa keyar Samanja suka nufi dakin da yammatan da aka kamo suke ciki, sai alokacinne Samanja ya lura dakyau, she daya daya cikin masu gadin kofarne ya shammaceshi suka hangoshi rabe abayan itatuwa, ya kewaye ta baya ya rutsashi, tabbas sai yanzu Samanja ya tuna da dadan kalaman budurwar tasa Suwaiba dayaji suna tashi acikin kwakwalwarsa, alokacin daya hangi dakin da suke ciki, babu shakka wan nan kururuwar zancen zucin kalaman soyayyar su suka mantar dashi a inda yake har wadan nan matasan suka sami nasarar hangoshi abayan itatuwa yana rabe. , Bayan sun isa kofar dakin, daya matashin dake tsaye bakin kofar shima rike da tasa bindigar ya taso da sauri ya tarbi gaban inda Samanja yake tsaye, cikin fushi da zafin rai ya gabzama samanja kan bindigar dake hannunsa afuska, nan take samanja ya kwalla ihu, lokacin da kan katakon bindigar ya hadu da hakoransa, jini yayi tsartuwa daga bakinsa, matashin farko wanda ya taso keyar Samanja, ya sake saita kan bindigar adaidai wuyan sa, yace cikin wata kakkausar murya, '' Daga ina kake kuma me yakawoka nan, ? Dan sandane kai ko soja, ko wanne irin jami'in tsarone, kuma ku nawane ina sauran?'' Samanja da radadin dukan bindiga ke ratsa tsakanin hakoransa, jini na zuba, ya amsa dakyar alokacin da ya lura daya azzalumin na shirin kara bugamai kan bindigar aka, yace cikin raunin murya ''Ni kadaine, nazo wajen sahibata ne Suwaiba wadda kuka kamo dazu daga kauyen kaimon kaura,'' Samarin biyu sukayi murmushi, alokaci daya suka sake daure fuska, sukace atare '' waya gayama tana nan da har zaka biyo bayanta?'' . Samanja yayi nishi sama sama, san nan yace ''Ni dakaina na ganku, adaidai kwanar shiga kauyen mu lokacin na biyo bayan zani gari nemanta, sai gata ta sauka amota, kamin mu hadu wasu mutum biyu suka shiga tsakinmu da mota suka daukota suka kawota nan, ina biye dasu'' Oh daya katon ya fada yana murmushin mugunta, yace ''dakyau masoyi, ka biyo masoyiyarka kenan, yayi kyau, yanzu bara ka isa gareta sai ka jira sakamakonku tare, kamin megida ya dawo,'' Katon ya sake takarkarewa iya karfinsa ya wanke fuskar Samanja da wani mahaukacin duka da hannu, nan take samanja ya fadi kasa sumamme, daga nan suka bude dakin suka jefashi, ya fada tsakar dakin ko motsawa baya iyayi, suka shaidama daya matashin dake ciki yana gadin yammatan, ''wan nan bakonkane, ka kula dashi dakyau Saurayin Suwaibane yarinyar da Su mubarak suka kamo dazu, inya farfado sai ka tsaya daga gefe kasha kallon soyayya'' Suka tintsire da dariya alokaci daya cikin isgilanci, ya ja kofar dakin suka kulle, suna dariya da mamakin yanda samanja ke tabbatar musu da wajen budurwarsa yazo ko tsoro babu amuryarsa, ''lallai wan nan masoyine'' suka fada atare suka cigaba da gadin da lura da matsin dake kadawa awajen. Bayan shudewar wadasu yan awanni, can Samanja yadan motsa dakyar fuskarsa cike da radadin dukan da gabjejen katon nan na bakin kofa yayi mashi dazu, ya juya yana kallo dakin dayake ciki dishi dishi yake lura da mutanen da ke cikin dakin, sai alokacin ya fara tuna halinda ya shiga kamin zuwansa gidan da abinda ya faru dashi bayan wani matsayin kato ya tasoshi da bindiga. Bayan dogon motsin dayayine, ya lura da wani kafcecen kato dake tsaye kansa rike da bindiga, yana kallonsa yana gyara rikon bindigarsa, dakyau Samanja ya mike zaune, san nan ne ya fara ganin duk abinda ke cikin dakin, wasu yammata ya gani zazzaune wasu atsaye sun cika dakin wasu suna tagumi wasu na kuka, adaidai lokacin ne, suka hada ido da masoyiyarsa Suwaiba dake makure can ajikin bango. Suwaiba ta runtumo aguje ta nufo kan Masoyinta Samanja tana kuka, Samanja ya kalli faskeken katon dake gadinsu, zuciyarsa cike da sake saken yanda zai iya mai kisan mummuke, sai da ya da sahibarsa na tunkaroshi san nan yaji wani karfi na shigarsa duk kuzarin sa ya dawo jikinsa, aransa ya fada ''dole sai yayi wani babban motsi don kubutar da kansa da masoyiyarsa daga yan yankan kan nan, kamar yanda yake zargi. Suwaiba ta fada jikin Samanja tana kuka, Samanja ya kalleta idonsa yayi jawur. . *Usman Auwalu zango* . MUHADU A WANI PART DIN NAGABA Tahanyar yin comments din ku zangane kuna taredani don kawo maku labarin cikin gaggawa . 07066055575 [10:57AM, 1/26/2017] Usman Auwalu Zango: BAKIN LISSAFI 11 - 12 . Ransa cike da damuwar ganin halin da rabin ransa take ciki, sai alokacin Samanja ya sake lura da katon matashin dake gadinsu, ya saita kan bindigarsa adaidai goshin Samanja yana jiran wani motsi ya sakar masa harsashin dake makare da bindigar. Samanja ya sa habar rigarsa yana Sharema Suwaiba hawayen dake zuba daga idanunta, san nan ya dubi sauran yammatan dake dakin kusan dukkansu yaran matane matasa kamar Suwaibarsa, can acikin ransa sai yaji tausayinsu ya kamashi, duk da rashin imanin da ya dade yana nunawa arayuwa, amma da zarar ya ga matashiyar budurwa yakan sassauta mata, saboda yana tuna tasa budurwar Suwaiba. . Yammatan duk sun zuba musu ido, suna kallon soyayyar masoya, adaidai lokacinne Samanja ya shammaci Faskeken katon nan dake rike da bindiga akansu, yasa gwiwar hannunsa ya gabzamai duka iya karfinsa adaidai kan gwiwar kafarsa ta dama, nan take katon ya kwallara ihu, cikin wata disasshiyar murya, ya zube da gwiwarsa yana duba inda samanja ya dokai da gudumar karfe kamar yanda yake tsammani, cikin zafin nama Samanja ya sake kaftamai duka adaidai dokin wuyansa, na nake ya sankare ya fadi ta baya bindigar dake hannunsa ta subucemai, suka kai wawa atare da samanja amma ba wanda yakai gareta, saboda yunkurin da faskeken katon yayi ya saka ya doki daidai kwugun Samanja, Samanja yayi baya taga taga, san nan lokaci daya dukansu suka zabura suka mike kowa na kallon juna suna huci. Faskeken katon ya zaburo a fusace, yayo kan samanja da niyyar yayimai shiga daya, ya kawoma samanja duka Samanja ya kauce dukan yabi iska, ganin haka katon ya runbabeshi ya daga samanja sama, zai buga da kasa, Allah yaba samanja sa'a ya riko wani karfe mai raga raga dake daga baya ta jikin windon dakin taga, katon yaja yaja samanja yaki sakin karfen, can katon ya fusata ya figa iya karfinsa adaidai lokacinne karfen windon ya finciko da karfin tsiya ya biyo hannun Samanja, Tundaga saman kafadar katon inda Samanja ke cin kasuwar Sama, Samanja ya yunkura iya karfinsa ya Bugama katon karfen dake hannunsa na windon dakin, nan take karfen ya lume akan mutumin, katon yayi wata kuwwa, Samanja yayi sauri ya toshe bakin matshin katon da tafin hannunsa, don ragema ihun karfin sauti. Lokaci daya katon yayi baya taga taga ya hade da jikin bangon dakin ya zube kasa yana nishi sama sama, jini ya fara cikin kasuwa afuskarsa, Samanja ya matsa kusa dashi yana bude ido dakyar yana kallon samanja dishi dishi, Samanja ya sake yunkurawa da duk iya karfinsa ya saukemai wani mahaukacin duka adaidai kan fuskarsa nn take katon ya fadi kasa asume baiko kara motsawa ba, samanya yayi murmushin mugunta can acikin ransa yace ko banza na rama irin dukan da yan uwanka sukayi min, Anyi babbar sa'a OGA mr marcus da yaransa da suka fita tun misalin karfe 2:30, don gayyato gyatumin matsoraciyar budurwa Ester, basu sha wata wahalaba wajen gane unguwar da mutumin yake Mr Oladinco, saidai sunyi rashin sa'a baya gida yaje kasuwa, inda katon shagonsa yake yana sana'ar sayar da safaya part na motoci. . Kai tsaye marcus da yaransa suka wuce can bakin tsohuwar kasuwa, inda mr Ola ke gudanar da sa'arsa, mr Oladinco tsohon bayarabene wanda ya dade da shigowa kasar hausa neman kudi, tun awasu shekaru can masu nisa, don haka ya samu karbuwa acikin kasuwancinsa yanada mutane sosai wadan da yake mu'amala dasu, date da yaran shago dayawa, da wadanda yaye ya kakkafasu awasu shaunan nasu nakansu, An tabbatar Mr Ola bashida ganin kyashi ko hassada akan kasuwancinsa wan nan yasa yama mai farinji, musamman ma awajen hausawanmu da suke rabawa yana basu bashi ko rancen kudi, wasu su dawomai dasu wasu kuma sai akiyama. Bayan marcus da tawagarsa sun gama nazartar katon bayaraben dake zaune daga kan wata kujera abakin shagonsa, sai marcus yacema yaransa ''ku jirani ina zuwa bara naje nasameshi dakaina,'' marcus ya fita daga motar ya nufi tulelen bayaraben yana washemai baki, bayan sun gaisa, marcus ya gabataimai da kansa, cewa shi malamine daga makarantar su Ester yarinyarsa, yazo don ya tafi dashine don ana menan iyayesu amakaranta saboda satar da akayi musu jiya, mr Oladinco ya nuna rashin amincewa yabi marcus saboda harkokin kasuwancinsu, amma yace zai tura yaronsa yayan ester kenan, wan nan yasa marcus tababa da maganar tsohon bayaraben, bayan marcus ya matsa don ganin lallai sai sun tafi tare da mr Oladinco, sai mr Ola ya fara kokonton wan nan tafiya wan nan yasa fara tseguntama abokan kasuwancinsa cewa shifa baima yarda da mutanen ba, wan nan yasa lokaci daya akayima su marcus ca da tambayoyi, inda aka dinga samun karon zantuka, Dakyar marcus da yaransa suka samu damar arcewa da motarsu bisa ganin mutane na yunkurin fada musu don nuna rashin yarda dasu. Anyi babbar sa'a OGA mr marcus da yaransa da suka fita tun misalin karfe 2:30, don gayyato gyatumin matsoraciyar budurwa Ester, basu sha wata wahalaba wajen gane unguwar da mutumin yake Mr Oladinco, saidai sunyi rashin sa'a baya gida yaje kasuwa, inda katon shagonsa yake yana sana'ar sayar da safaya part na motoci. . Kai tsaye marcus da yaransa suka wuce can bakin tsohuwar kasuwa, inda mr Ola ke gudanar da sa'arsa, mr Oladinco tsohon bayarabene wanda ya dade da shigowa kasar hausa neman kudi, tun awasu shekaru can masu nisa, don haka ya samu karbuwa acikin kasuwancinsa yanada mutane sosai wadan da yake mu'amala dasu, date da yaran shago dayawa, da wadanda yaye ya kakkafasu awasu shaunan nasu nakansu, An tabbatar Mr Ola bashida ganin kyashi ko hassada akan kasuwancinsa wan nan yasa yama mai farinji, musamman ma awajen hausawanmu da suke rabawa yana basu bashi ko rancen kudi, wasu su dawomai dasu wasu kuma sai akiyama. Bayan marcus da tawagarsa sun gama nazartar katon bayaraben dake zaune daga kan wata kujera abakin shagonsa, sai marcus yacema yaransa ''ku jirani ina zuwa bara naje nasameshi dakaina,'' marcus ya fita daga motar ya nufi tulelen bayaraben yana washemai baki, bayan sun gaisa, marcus ya gabataimai da kansa, cewa shi malamine daga makarantar su Ester yarinyarsa, yazo don ya tafi dashine don ana menan iyayesu amakaranta saboda satar da akayi musu jiya, mr Oladinco ya nuna rashin amincewa yabi marcus saboda harkokin kasuwancinsu, amma yace zai tura yaronsa yayan ester kenan, wan nan yasa marcus tababa da maganar tsohon bayaraben, bayan marcus ya matsa don ganin lallai sai sun tafi tare da mr Oladinco, sai mr Ola ya fara kokonton wan nan tafiya wan nan yasa fara tseguntama abokan kasuwancinsa cewa shifa baima yarda da mutanen ba, wan nan yasa lokaci daya akayima su marcus ca da tambayoyi, inda aka dinga samun karon zantuka, Dakyar marcus da yaransa suka samu damar arcewa da motarsu bisa ganin mutane na yunkurin fada musu don nuna rashin yarda dasu. . Tunda suka fito garin basu zame ko onaba sai gidan gonar da suka boye yammatan nan, cikin damuwar aikinsu nason baci akaron farko, Da sauri marcus ya nufi dakin da suka tara yamatan don fara tunanin mataki na gaba, amma abinda suka riska adakin yafi bashi tsoro akan abinda suka baro agari, dakin ba kowa sai yammata biyu, Suka rage Ester da kawarta sai katon dake kwance kasa asume, cikin kunar rai marcus ya tambayi yammatan wayayi wan nan aikin, ? Cikin rawar murya sukace '' samanjane'' marcus ya tambaya waye kuma samanja? Alokaci daya atare sukacemai saurayin Suwaiba ne, sun tafi kaimon kaura tare. Bayan samanja ya ga faskeken katon nan ya fadi kasa asume, bayan sun raba hammata da gwada karfin kwanji, cikin sauri ya juyo ga tawagar yammatan dake dakin suna kallon gumurzun daya faru atsakaninsu, yadan saurara kadan kozaiji wani motsi amma shuru sai karar dukan zuciyarsa data sauran yammatan, wan nan ya tabbatar mai da sauran masu gadin dakin dake waje suna nesa da kofar kenan shiyasa basu iya jiwo fadan faman da sukayi da maigadin dakin aciki ba. Da sauri samanja ya karika jikin windon dakin wanda tuni kofar sa abude take wayam, saboda babbake katon karfen rodin dake jikin windon da sukayi alokacin da suna gumurzun, bayan ya dan leka kansa daga waje yayi nazarin bayan dakunan wanda dajine sai gonaki dake can sun tafi fululu. . Samanja ya juyo dakin da sauri ya kira Suwaiba dake tsaye daga bayansa, yace to lokacin gudu yayi, maza ki haura nan mu kama hanyar gida, cikin azama samanja ya kama indon ya dira daga waje, ya juyo da sauri ya tallafe masoyiyarsa Suwaiba ya direta san nan ya kama hannunta har sun fara gudu, sai Suwaiba kalleshi tace cikin kasa kasa da murya, ''habibi sauran fa suma yakamata ataimaka musu,'' samanja ya kalleta yana kokarin share zufara dake tsatstsafowa daga goshinsa, yace '' haba habibi muyi ta kammu kawai, suma kowa tasa ta fissheshi'' Suwaiba tace '' a a habibi kawayenane fa ataimaka musu'' Cikin zafin nama samanja ya dawo bakin tagar da gudu, yace cikin karamar murya, ''duk wadda ke da shirin tafiya tayi maza mu runtuama kamin azzaluman nan su dawo'' Nan danan yammatan suka fara rububin bin bayansu, duka suka fito sai wasu yamma biyu ne basu bi bayansu ba, ester ce matsoraciya da kawarta, nan take samanja da yammatan suka runtuma cikin daji asukwane zukatansu cike da zullumin haduwa da wasu daga cikin muggan yan ta addar. Bayan doguwar tafiya ta ratse, da bin kwazazzaban dazuka can sukabulla wani kauye dake bakin hanya, mai suna Kwanar gurjiya, daga nan samanja ya ja yammatan suka boye abayan wani ginin tsohon masallaci daya fara rushewa, san nan ya fito bakin hanya yana tarbar musu motar zuwa Kaimon kaura. PART 14 kuriqayin comments don insan kuna tare dani [11:35AM, 8/27/2016] WHATSAPP N0 07066055575: BAKIN LISSAFI 14 . Ko minti biyu bai hadaba abakin titin ya hango wata tsohuwar motar akori kura, tundaga nesa ya ganeta motar Alhaji Madu ne sarkin fawan kaimon kaura da kewaye, yadawo cin kasuwa, samanja yayi sauri ya dagamai hannu, tundaga nesa shima yafara kokarin lalubar birkin motar don samun damar tsayawa adaidai inda ake tsaidashi, domin azatonsa, wani bafullatanine yake son sayar masa da maraka don ya hangi wata sanuwa dake kiwo daga cikin wata gona adaidai bayan samanja . Bayan tsohuwar motar ta tsaya dakyar, samanja ya runtuma asukwana ya shaidama Sarin fawa halin da suke ciki, daga nan yayi maza ya kira yammatan suka cika bodin motar daganan Alhaji madu sarkin fawa yaci gaba da caccakama motar giya suka nufi kauyesu kaimon kaura tare da tawagar yammatan. . Tunda yammatan nan biyu Ester da kawarta, suka labarta ma mr marcus guduwar samanja ya yammatan nan, hankalinsa ya dugunzuma ya tashi, domin yana da tabbacin aikinsa ya koma baya kuma da'alama yanason baci, cikin kunar rai yayo waje daga dakin ya nufi inda kattin nan biyu suke tsaye nesa da kofar dakin suna gadi, cikin zafin nama ya wanke fuskokinsu da wani zazzafan mari san nan cikin fada yake tuhumarsu da sakacin barin yammatan nan su gudu. Dakyar mr marcus ya iya fahimtarsu kan cewa wani saurayin wata budurwane aciki yazo tafiya da ita shine suka kamashi suka hada dashi adakin, suna nan waje suna gadi basu da labarin abinda ya faru acikin daki. Marcus ya juya cikin fushi ya nufi motarsu batare da yacema kowa kalaba, aransa yana fadin koda bala'i sai yaje wan nan kauye ya dawo da yammatan nan dama duk wanda tsautsayi yasa yaji labarin satar dakai adaren jiyaa amakarantar yammatan. Ganin ya wuce baicema kowa kalaba, ya saya yaran nasa bin sawunsa, da sauri suma suka fada motar, wan nan karon mr marcus da kansa ya figi motar afusace ya cilla da gudun bala'i kamar an harba kibiya suka nufi kauyen kaimon kaura da niyyar saidai ayita ta kare. . *** *** *** *** . Bayan Alhaji Madu sarkin fawa ya isa kauyen kaimon kaura, tun akan hanya kamin su karika Samanja ya sanar dashi cewa in ya isa ya wuce kai tsaye zuwa gidan me unguwa Malam tajo, don mika sauran yammatan gareshi san nan anemi garuruwansu amaidasu ga iyayensu, Ai kuwa haka akayi bayan shigar tsohuwar motar akori kurar kauyen da misalin wajen karfe hudu saura na yamma, sarkin fawa bai faka ako inaba sai daidai bakin kofar gidan me unguwa malam Tajo, saidai anyi rashin sa'a me unguwa baya gida yaje kewaya wata fadamarsa dake can dausayi, inda yayi rake awakai na yawan zuwa yimai barna, amma dai babban dan mai unguwa na nan wani sangwamemen kato girman kauye mai suna Sammani, wanda suka iske zaune akan wani gungumen icce yana hutawa yau baije yammaci gonaba duka mayen gonane. Sammani babban dan sarkin noma shi ya shigar da yammatan gidansu, tare da Samanja da suwaiba, akayi musu shimfida atsakar gidan suka zazzauna, daganan sarkin fawa ya wuce gida samanja da sahibarsa suwaiba ma duk suka nufi gida da niyyar sai me unguwa Tajo ya dawo gona zuwa magariba sai suzo amaida yanda akai. Sammani dan me unguwa bai cika wayau sosai ba, giman jikin ne kawai saida masifar karfi kamar shara'a, amma dai dolo dolo ne, nan da nan ya fita cikin kauyen wata majalisa da wasu matasa zauna gari banza abokansa suke yawan haduwa wadanda basason zuwa gona yammaci, sai zaman kashe wando gardamar kwallo da wasan karta da da kafsa ta kaddama akan Ali nuhu da Adam Zango wayafi wani tashe da iya fim, da kuma wasu daidaiku acikinsu da sukaje birni suka waye har suka fara dan daba shan taba, ya shaida musu cewa gidansu anyi bakin yammata, daga birni yanzu yanzun nan suna nan sun cika gidan. Cikin azama tawagar samarin zauna gari banza suka runtuma suka nufi gidan me unguwa don kowa ya zabi wadda yake so, Sammani dai shi har ya kama wadda yake so wata siririyar budurwa doguwa fara yake so daya dafa cikin tawagar yammatan sunan ta IHSAN. . Tunda Sammani yajawo tawagar abokansa, suka nufo gidansu don kowa ya duba budurwar da yakeso, sammani yana gaba saura na biye dashi abaya, da alama kowannensu zuciyarsa na cike da iya shege da shakiyyanci irin na matasan kauye. Yan mintina kadan yakaisu gidan mai unguwa tajo dake can kusa da tsohuwar primary dake kusa da bayan gari, inda kaitsaye batare da bata lokaci ba Sammani yashiga gaba suka bishi cikin gidan, azaune suka tadda yammatan suna hutawa cikin al'ajabin halin da suke ciki, sammani ne yafara nuna wata sambaleliyar budurwa yace yana washe baki ''Ni ga tawa nan, kaima Dogara ka zabi taka'' ya tabo wani gajeren kato baki mai siffar yan dambe dake kusa dashi. . Wanda Sammani ya kira dogara ya washe baki yana kallon kyawawan yammatan, yace ''waccan nakeso'' shima ya nuna wata farar budurwa siririya dake daga tsakiyar yammatan azaune, daga nan kowa ya nuna wadda yakeso, cikin ranshin wayau da dolonci na bakauyen da ya dade bai shiga gari ba. . Like Social media Hausa Novels [11:36AM, 8/27/2016] WHATSAPP N0 07066055575: BAKIN LISSAFI 15 . Hankalin yammatan yafara tashi ganin samarin kamar suna shirin fada musu, sun kewayesu sunata musu wawanci, zukatan yammatan ya cika da zullumin Allah sa ba gudun gara sukayiba suka fada gidan zago. Ganin matasan da gaske suke shakiyancin nasu, yasa mahaifiyar sammani wata dattijuwa mai suna Mero ta fito dakin girki da gudu rike da mucciyar tuka tuwo ahannu, ta nufo samarin tana surfa musu zagi, akan me zasuzo su takurama bakin yammata. Tun kamin matar ta kariko wajen matasan suka runtuma sukayi waje da gudu, adaidai soron gidanne sukaci karo da mai unguwa ya dawo gona yana tafe yana gungura wata tsohuwar akwalar kekensa yayo ciyawar dabbobi, wani matashi mai suna Ya'ulle shine ya banke keken mai unguwa garin gudu ya shalllake shi suka fada wata gonar dawa dake daga bayan gidan mai unguwa suna dariya. Bayan me unguwa ya kariko cikin gidan shima tundaga bakin kofa yayi tozali da yammatan dake zaune abakin turakarsa an baza musu wani tsohon tamfal dinsa na fyadin shinkafa suna zaune, bayan me unguwa ya jingine akwalar kekensa akusa da rumfar awakinsu, sai yayo tsakar gidan yana kwalama mero kira uwar gidansa, ''Mero baki mukayine'', yana magana yana kallon yammatan, uwargidan mai unguwa ta fito daga dakin girkin idonta yayi jawur da alama wuta take hurawa hayaki ya cika mata ido, ta fyace majina da gefeb zaninta san nan ta kalli me unguwa dake tsaye tsakar gidan tace '' bakine daga birni dazu Samanja yazo dasu nan gidan yace bayan sallar magariba zaizo kuyi magana, shida Sarkin fawa suka zo gidan nan dazu kana gona'' Me unguwa ya dubi yammatan alokaci daya yace yana washe musu baki, ''Sannunku da zuwa fa dafatan anzo lafiya ya birni?'' yammatan suka amsa atare ''lafiya kalau'' daga nan ya shige dakinsa, yayi alwalar sallar magariba ganin lokaci ya kawi jiki , san nan ya fice daga gidan ya nufi masallaci dake can tsakiyar kauyen wajen babban dandali. . *** *** *** Tunda Marcus ya kamo hanyar kaimon kaura bai saurara ma motar nan ko sau dayaba, caccaka mata wuta kawai yake yana sheka gudu kamar zasu tashi sama, cikin kankanin lokaci suka shigo kaimon kaura, saidai lokacin duhu ya fara domin anata kiran sallar magariba, amasallatan dake kauyen, acan bayan gari suka ajiye motarsu daga gefen wata gonar masara wadda take gab dafara fiddakai, san nan ya ummarci sauran yaransa da su jirashi abakin mota zai shiga binciken Samanja, alokuta da dama Marcus yafison yin irin wan nan aikin shikadai domin yafi yarda dakansa akan kowa, don haka cikin yakini ya kutsakai cikin garin yana tafiya yana lura da mutanen dake wucewa kusa dashi, can ya hangi wata yarinya tana ta sauri ta dauko nika awani inji, tan saurin takai gida don kada suyi daren tuwo har magariba tayi, da sauri Marcus yasha gabanta yana mata murmushi yace ''kanwata kina sauri ko ni Abokin Samanjane daga hayican nake, ko kinsan gidansu'' ? Yarinyar tadanja kadan ta tsaya san nan ta kalli Marcus dake gabanta atsaye, tace ''Aiduk kauyen nan ba wanda baisan Samanja me dawa ba, kaga gidacan mara kofa'' yarinyar ta nuna wani gida dake can nesa dasu, samanja ya hangi inda yarinyar ke nunawa yace ''kwarai na hangi gidan gida mai jar kasa ko?'' ya tambayi yarinyar tace ''yawwa nan to nan ne gidansu Samanja dazun nan ma naganshi ya wuce tare da mutumiyar tasa'' samanja yayi sauri ya tarbi nunfashin yarinyar alokacin da take kokarin wucewa, yace ''Suwaiba ko''? Yarinyar tace tabbas ai baida wadda tafita, don yana iya komai akanta. . Mr marcus ya juya ya nufi gidan da yarinyar ta nunamai, zuciyarsa cike da tabbacin ya gane Gidansu Samanja, tun kamin ya karika kofar gidan ya rakube ajikin wata kwana, yana jiran yaga wazai fito daga gidan, bayan wasu yan mintina kadan baiga kowa ya fito daga gidanba, sai ya samu wani almajiri dake yawon bara da maraicen, yazo zai wuce ta inda yake rabe, Marcus yace da yaron almajirin ''kasan can gidan?'' ya nuna gidansu Samanja Al'majirin yace ''nasani gidan su Iroro ne'' waye kuma iroro'' marcus ya tambayeshi, ''kanin Samanja nem shine abokina'' ''dakyau Marcus yace yana kallon yaron '' yanzu maza kaje ka kiramin yaron kaga naira Hamsin nan zan baka, marcus yazo sabuwar naira hamsi ya mika ma Al'majirin ahannu. Nan da nan saiga Al'amjiri ya fito tare da wani yaro sa'ansa, yacema marcus dake rakube abayan wani gini, ga iroron'' Marcus yayi murmushi yace yawwa ''dan malam na gode zaka iya tafiyarka'' Marcus ya kalli yaron da ake kira iroro yace yana murmushi haryanzu a fuskarsa, ''ina yayanka Samanja'' Yaro yace ''ai yafita tun dazu yana gidansu Suwaiba,'' marcus yace dakyau, ai abokinane, wasu bakin yammata dayazo dasu dazu suna ciki ko?'' yaron yace '' a a ai banan yazo dasu ba suna gidan mai unguwa, can yabarsu tunzu, sai mai unguwa ya dawo gona, wadanda yazo dasu daga birni ko''? Yaron ya tambaya, Marcus ya girgiza kai yace ''ok inane gidan mai unguwan,'' Yaron yace ai yanacan kusa da fita gari ta nan hanyar, ya nuna inda marcus ya fito. Mr marcus yace na gane, amma muje karakani gidan zan baka naira hamsin kasha dan tamatsitsi, yaro ya washe baki jin zan samu kudi, yace muje in rakaka. mr marcus da yaron sun isa kofar gidan adaidai lokacin da ake tayar da sallar magaruba abban masallacin kauyen dake can dandali, suna jiwo karar lasafikar masallacin wani ladani mai zakin murya sai rangada kabbara yake, wan nan ya tabbatarma da Mr marcus duk manyan gidan basa nan don haka nan danan yacema yaron nan ''maza ka shiga kace ance wai yammatan nan da sukazo suzo ana kira inji mai unguwa za aje dasu hayin Babba da jaka, gidan hakimi'' yaron yace to ya fada gidan, da sauri, ganin yaron ya fada gidan yasa marcus sauri ya fada daga cikin zaure ya rabe abakin kofa ya zaro wata karamar bindiga. Mintina kadan sai ga yaron tare da tawagar yammatan sun fito lokaci daya, nan danan marcus ya rutsasu da bindigarsa yana tsare musu ido, yace cikin kakkausar murya, duk wadda tayi babban matsi saina harbeta nan kusa da bayan garine bawanda zaiji kumuje waje, marcus ya tasa yammatan nan agaba, cikin matsanancin tsoro da fargaba, yammatan suke bin ummarninsa, marcus ya tasasu har bakin inda suka aje motarsu, san nan sauran yaransa suka fito da sauri suka tarbi oga tare da yammatan, san nan suka tasa keyarsu zuwa cikin motar. mr marcus yayi murmushin mugunta, bayan yaga yammatan sun gama shiga motar san nan shima ya shiga mazaunin direba yaransa suka fada motar yajata asukwane yayi gaba yana dariya. . Bayan Mr Marcus ya zafgama doguwar motar giya, ya fita asukwane ya keta da gudu ta cikin wata gonar waken suya da tayi yabanya laho- laho, yafada wani kwarin kunya da ruwa ya taru, ya taka motar ruwa da tabo ya fallatse ajikin gayyen waken suyan dake gonar, gurin yayi kaca- kaca, ya samu yakoma kan kwazazzabon hanyar dakyar, san nan ya sake taka motar da gudu. yammatan daya sake sacewa cike da motar kowacce ciki ya duri ruwa, sai faman zare ido suke zuciya cike fal da fargaba, yaransa na rike da bindigogi suna gadin yammatan tare da lura da motsin kowacce yarinya, cikin shirin kota kwana ga duk yarinyar da tayi wautar kwarma ihu ko kokarin dira ta windo, da sauri harsasai zasu ratattaka kanta ko daidai zuciyarta. Bayan marcun yaci gaba da tsulama motar wuta tare da jefa mata giyoyi barkatai, don sauri tare da kokarin barin yankin karkarar ta Kaimon kaura, kamin a ankara da barnar da sukayo, can bayan ya wuce wasu gonakin shinkafa guda biyu dake makotaka da juna, alokacin duhun dare yafara bisa rashin zato sai yaran marcus sukaga yaci wani mahaukacin burki, dakyar motar ta tsaya, saida ta hankada kamar zasu fadi, san nan cikin zafin nama ya dauke kan motar tafada wata gonar makani, yayi rubus yasake dannawa aguje yakoma ta hanyar da suka fito ya nufi kaimon kaura gadan gadan. Yaran marcus da yammatan nan cikin matsanancin mamaki suka dubi marcus dake ta kokarin karama motar giya, dakyar mubarak ya hadiye mamakinsa ya tambayi marcus, ''Oga ina kake da nufin zamu koma, ? Ko ka bace hanyane,'' batare da marcus ya kalli inda suke ba, yace yana kokarin ketare wari rafi da ruwa ya taru akan hanya, ''Munyi tuya mun manta da albasa, SUWAIBA da saurayinta SAMANJA Tabbas izuwa yanzu Samanja ya gama sanin inda kan zancen ya nufa, kunga kenan shima yana cikin komar binciken mu'' Dayawa cikin yaran nasa sunyi kokarin ankarar da marcus kan cewa yayi hakuri su tafi da wadanda suka kama, amma ya nuna musu ya fisu sanin aikin don haka dole suka hakura, suka rabu dashi don ganin rai zai baci. Wan nan shine babban kuskuren marcus, dayasan abinda zai faru dashi in yakoma kaimon kaura da niyyar taso keyar Suwaiba da Samanja da sam bai yunkurin aikata hakan ba, dazaifimai sauki ya sauke yammatan ya tafi ofishin yansanda ya mika kansa amatsayin barawon kayan mata, ahukuntasa daidai da satar dayayi, akan abinda ke jiransa akaimon kaura. . *** *** *** Bayan an sallame sallar magaruba, amasallacin tsakiyar kauyen Kaimon Kaura, da sauri mai unguwa Tajo ya shafa addu'a batare da ya jira an yi addu'a atare ba kamar yanda aka saba, ya fito kofar masallacin ya kira ladanin masallacin Malam rabu'u, ya dan labartamai halin da ake ciki da yammatan da suka bakunci gidansa ayau, yace in an yi addu'a ya shaidama liman abinda ke faruwa su sameshi agida yayi gaba. Tunkamin mai unguwa ya karika bakin kofar gidansa ya hangi Tasi'u gardi tsaye akofar gidan, daya daga cikin dogaran mai girma Hakimin gundumarsu ne, Alhaji Baballe dake can kauyen TANDU, wani bakin katone kakkarfa, yana tsaye yana jiran zuwan Mai unguwa, me unguwa ya tambayi kansa, wa kuma ya je har TANDU da wan nan yammaci ya labartama hakimi zuwan yammatan nan, har ya taso dan aike. Bayan me unguwa ya karika kofar gidan suka gaisa da Tasi'u Gardi, tasi'u ya sanarmai da cewa mai girma Hakimi yaji labarin anyi wasu bakin yammata daga birni ayammacin yau, shine ya turoni danazo na tafi dasu can don bin ba'asi yace ka shirya mutafi tare can TANDU yanzu yanzu. . Like Social media Hausa Novels [11:13AM, 8/28/2016] Usman Auwalu: BAKIN LISSAFI 17 . Me unguwa bayanda ya iya da umarnin Hakiminsa Alhaji Baballe, dole ya fada gida da sauri don tattaro tawagar yammatan su nufi kauyen Tandu don cika umarnin hakimi, bayan yan mintina kadan da shigar Me unguwa gida da niyyar tattaro yammata suzo su kama hanyar Zuwa kauyen TanDu,inda matsugunin Hakimi yake, saigashi kuma ya fito da sauri jikinsa ba kwarai adaidai lokacinne malam Rabi'u Ladanin kaimon Kaura da Malam Dan Haru limamin Kauyen suka iso kofar gidan me unguwa, kowan nensu sanye da wasu zunbula zumbulan manyan giguna malum malum, sunata buya buya, su ga manyan gari anzo jin yanda al'amarin yammata yakasance. . Me unguwa tajo yayi turus agaban Tasi'u gardi jikinsa na tsuma, ya labarta musu lallai wani yazo ya tafi da yammatan nan amma baisan ko waye ba, ancemaidai wani yaro aka turo kanin Samanja mai dawa, don haka bamuga ta zama ba' suka juya su duka suka runtuma suka nufi gidan su Samanja. Tunda mr marcus ya juyo kan motar nan asukwane ta nufo kauyen kaimon kaura, da tunanin tattara SAMANJA da sahibarsa SUWAIBA ya sake arcewa dasu, ashe bai sani ba wan nan shine kuskure na farko daya fara aikatawa aduk cikin aikinsa daya kwashe tsawon wunin yau yana aikatawa. Saida ya kusa shigowa kauyen san nan ya rage gudun motar ya sulala ahankali ya nufi gefen hanya daidai wata gonar Masara ya faka motar san nan ya kashe duka fitulunta, ya fito da sauri yasa yaransa suyi gadin yammatan san nan ya juya da sauri ya nufi cikin kauyen shikadai gidansu Samanja ya nufa gadan gadan, da tunanin inbaisamesu agidanba ya wuce gidansu Suwaiba kaitsaye, yana soke da karamar bindigarsa acikin wando, zuciyarsa cike da yakinin itakadai zata iya tattarai mutanen kauyen nan kaf yatafi dasu duk inda yakeso. *** *** *** ** Kofar gidansu Samanja me unguwa tajo ne tare da Tasi'u gardi dogarin hakimin Kauyen Tandu Alhaji Baballe, sai babban limamin kaimom kaura, tare da malam Rabi'u ladanin kauyen, sun tura yaro gidansu Samanja kenan don akirashi, sai ga tawagar matasan kauyen nan sun iso kofar gidan, Sammanine tare da abokansa, wadanda suke son yammatan nan, sun koma gidan su Sammani akace musu an tafi da yammatan sune suma suka biyo bayan yammatansu, don wani kaura acikin su mai suna Darda'u dayace yana son wata kakkaurar budurwa acikin yammatan yace shi ba ruwansa zai iya kashe mutum akan matashiyar budurwar. Cikin rudani Samanja ya fito daga cikin gidansu, jin kiran me unguwa agidansu da wan nan lokaci, yasan wata kila maganar yammatan nan nan ne, amma ai me unguwa aikowa ya kamata yayi akirashi ba'ace gashi nan yazo da kansa ba, bayan Samanja ya fito me unguwa ya fara tarbarsa da zance ko yammatan nan suna gidansu shi ya tura kaninsa iroro ya kirasu, samanja yayi turus agaban Me unguwa hankalinsa atashe yace ina ai bai kara komawa ta kansu ba, shi yana gidansu Suwaiba suna tare, nan danan aka kira Iroro kanin Samanja aka tambayeshi yaushe Samanja ya turaka ka kira bakin yammatan nan? . Iroro yayi narainarai da idanu yana kallon mutane, suka hada ido da jajayen idaun Tasi'u Gardi Dogarin mai girma hakimin Tandu, nan da nan yaji gabansa ya fadi, yace ''wani bakone yazo yacemin abokinka ne,'' iroro ya nuna Samanja, ''shine yace nakaisa gidan me unguwa don ya ga yammatan bayan na gayamai suna can shine mukaje nakirasu nadaiga yayi bayan gari dasu wajen gonar Dan Ali mai shago'' Nan take mutanen dake wajen suka fahinci lallai wani yazo ya sace yammatan, batare da bata lokaciba guri ya cika da mutanen gari ana labarin barayin yammata sun shugo gari sun sace wata tawagar yammata sukun da guda. Wani dattijo mai suna Dallami ya fadi cewa shi yaga wata bakuwar motar gefen magaruba ya dawo gona, adaidai nan bayan gari, kuma babu shakka ya hangi kan wata budurwa aciki saidai bai sani ba sunada yawa shidai mace daya yasamu nasarar hangowa, nan take Me unguwa ya kira hakimi ya shaidamai halin da ake ciki san nan ya nemi taimakon yandoka acikin aikin atarba kauyukan dake yankin, batare da bata lokaciba hakimi ya sanar da D P On yansanda dake yankin aka taso motar yansanda uku suka nufo Kauyen kaimon kaura. . Like my new page Social Fresh Hausa Novels [9:11PM, 8/29/2016] Usman Auwalu: BAKIN LISSAFI 18 ****** KARSHE ****** . Batare da bata lokaciba matasa suka zabura asukwane tare da su me unguwa akayi hanyan bayan gari inda akace an ga bakuwar mota dazu, aka barbazu, ana neman yammatan da barayinsu, wani matashi mai suna Jallo yazo wucewa ta kofar wani gida kenan yanadauke da wani katon icce sukaci karo da wata tsohuwa tacemai ''acan kwanar naga wani mutum da alama bakone, yana ta rabe rabe ku bincikashi don ni ina zarginsa'' Jallo yasha kwanar cikin sanda ya hangi dishi dishin kayan marcus arabe jikin wata katuwar bishiyar kuka ya sadada ahankali, yabi ta bayansa saidayaje dab dashi san nan ya damki wuyan rigarsa, marcus ya juyo da sauri suka hada ido, tabbas bakone jallo ya fada yana cije baki kamin mr marcus ya ankara saidai yaji saukar wani abu akasan hancinsa jini yayi tsartuwa hakoransa biyar suka tashi sama cikin iska, san nan wani radadi ya gauraye ilahirin bakinsa zuwa kai, jjini yafara sartu agaban rigarsa. Ko dakika biyar ba'ayiba, Marcus na shirin yunkurin guduwa yaji wani abu mai kaifi ya dube asaman kafadarsa, sai da wani zafi ya biyo baya san nan ya ankara ashe wuka Katon dake kansa ya lumamai akafada, yafadi kasa nan take yana kwarma ihu, daga nan katon mai suna Jallo ya saba marcus awuya ya nufi bayan gari dashi inda yake jiwo hayaniyar mutane, Can abayan gari ba'asha wuyaba wajen gano wata doguwar mota fara, an boyeta wakusa da wata gonar masara, . kuma tabbas yammata ne aciki, amma an kasa kusantar motar saboda karar harbin bindiga da akeji yana tasowa daga motar, barayin har bindiga garesu inji wani matashi, andan dade ana cirko cirko abayan garin kamin daga baya akasamu wasu matasa mutum Uku sukayi kukan kura suka afkama barayin, ana tsammanin samarin sunada maganin bindiga, sai bayan sun rufar ma barayin ne, san nan sauran tawagar matasan dake wajen suka mara musu baya, nan take sukayima barayin kofar rago, aka ratattake su da dukan itace, ana tsammanin wasu daga cikima sun sheka bar zahu. Can bayan wani dan lokaci ana tunanin abinyi, sai aka hango wani Sangwamemen kato mai suna Jallo ya dauko wani mutum akafada ya nufo inda mutanen suke, saida ya kariko wajen san nan ya shaida musu cewa acan bayan gidan Tanko mai gatari ya ga matashin rabe jikin wata kuka yana lambo, shine ya samu nasarar tarwatse shi da duka, ya jefar da marcus akasa ya fada jikin sauran yan'uwansa. An samu an firfito da yammatan daga cikin motar ana cikin juyayi da tuajjabin abinda ya faru, sai ga motocin yansa guda uku daga hayin Tandu sun iso wajen da abin ke faruwa, nan take matasan da sukayi aika aikar, suka sulale suka bar wajen don tunanin kada yansandar su zafga kame akan mai uwa da wabi, daga nan suka kwashe marcus da sauran yaransa suka nufi asibiti dasu dake can birni, bayan tafiyar yan sandan ne, me unguwa tajo da sauran dattijan kauyen suka tattara yammatan nan kaf suka nufi Tandu fadar mai girma hakimi Alhaji Baballe, don bin ba'asi da yunkurin maida yammatan ga iyayensu. adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *