Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Wednesday, March 22, 2017

Bazan barshi ba

adsense here [11:17PM, 1/25/2017] Ummi Ya: ```🔮BAZAN BAR SHI BA!🔮``` _[9/25/2016]_ *Na Billy giro😊* 🔮🔮🔮🔮񛠊 _*page 1*_ Rayyanat! Rayyanat!! Rayyanat!!! Er 16 yrs ce ta fito da gudu tana fad'in "Na'am Baffanah" Shiru baffan nata yayi yana mai kallon Rayyanat wacce ta kasance chocolate ba qiba ba rama tana da kyau daidai gwargwado tana sanye da riga da zane bara da bana sae dankwalin kanta da shima ba kalarkayan jikin ta bane ga zanen jikinta duk gabad'ayan sa dashi ne ba masoka tsintsinya gashi ta riqe wani gurin da ya yage bata son aga jikin ta yace"Rayyanat baki sami allura da zare bane wannan karon? Abba ban samu ba naje suka ce baza su ara min ba sun gaji da siya ina qare musu zaren"cikin muryar kuka ta qarasa maganar ,Baffan ta yace"kar kiyi kuka Rayyant inshaAllah yau idan mai gari ya biyani kud'in noman da nake masa zan saya miki allura da zare domin ki huta da aro maqota kinji"to Baffanah na gode Allah yasa ayi nasara fiye da kullum" yace "Amin Rayyant, zan tafi ki kula da kanki banda yawon maqota"inshaAllah amma Abba yau baka so na raka ne?Rayyanat ta yaya zaki fita bayan zanin ki ya yage ga samarin da ke dandali a tsakiyar gari"Haka ne Baffa Allah kiyaye hanya"Amin Amin. Daga haka ya fita rataye da fartanya kan kafad'ar shi inda Rayyant tabi mahaifin nata da kallo wanda shima tufafin jikin sa duk sun tsufa sun tamure. sae da ta daina hango shi sannan ta koma d'aki tayi zaune tana qarewa d'an akurkin d'akin ta kallo wanda ba wasu kayan kirki a ciki face d'an kunshin tufafin ta da baza su wuce kala biyu zuwa uku ba sae tsofuwar tabamar da take kwanciya da wani pillow akai mai kama latsatstsen biredi sae gidan sauro da aka dunqule shi aka soka jikin taga sae wasu kwallaye guda biyu da ke cikin d'akin da bansan meye a cikin su ba. Tana cikin qarewa d'akin kallo cikin ta ya shiga qugi sbd yunwar da ke addabar ta wacce tun safiyar jiya da suka ci abinci ita da Baffan ta har yau washe gari basu sake samun abinda suka ci ba. Kwanciya tayi ko zata samu bacci ya d'auke ta kafin Baffan ta ya dawo amma yunwa ta hana ta bacci kamar yanda tayi fama a daren jiya wanda sae da ta cika cikin ta da ruwa ta samu tayi bacci haka ko yanxu tashi tayi taje waje gurin randar ruwa ta cika cikin ta tap ta koma ta kwanta . Har bacci ya soma d'aukar ta ne taji sallamar wata qawar ta mai suna "Sarat" Sae da Rayyanat ta amsa mata sallama sannan ta shigo . Yarinya ce doguwa er sililiya baka wacce ita ma tana da kyaun ta dai dai gwargwado zama tayi tace"Rayyanat kiyi haquri fa tun jiya naso ace nazo amma shiryen shiryen tafiyar da muke yi na komawa Birni bai barni ba " D'an guntun murmushi Rayyanat tayi taji kamar ita ce zasu je Birni ita da Baffan ta sbd ta kasance tana mugun son zuwa Birni amma ko sau d'aya bata ta6a samun zuwa ba. Sarat ta miqa mata wata er baqar leda wacce ake kira cefanen mutum d'aya tace"dan Allah kar ki ce baza ki kar6a ba sbd nasan halin ki kuma ban saya miki don wata manufa ba sae don nasan kina bala'in son rogo inda har ka kasuwa naje na saya miki amma kiyi haquri nasan ba kya son haka " ba komai Sarat a yau zan kar6i kyautar ki sbd zaki tafi ki barni ban kuma san yaushe zamu sake had'uwa ba nagode amma yaushe ne zakuyi tafiyar ?a yau d'in nan kuma a yanzu shiyasa na baki haquri kan rashin zuwa na tun jiya nima ban so haka ba wlh...kar ki damu domin nafi kowa sanin yanda kika damu dani shiyasa a kullum bani da wata qawar da ta fiki...Uhm na gode Rayyanat ni zan tafi su Abba na a bakin qofar gida da mota suna jiran fitowa ta . Nan Rayyanat ta tashi suka fito inda Rayyanat ta russuna cikin ladabi ta gaida iyayen Sarat kafin wani d'an matashin saurayi ya fito a cikin motar wanda sak Sarat ce da alama yayanta ne. Da sauri Rayyanat ta duqar da kanta qasa cikin jin kunya tana d'an kame kame gayen yayi murmushi yace"ako yaushe ina sonki Rayyanat ba kuma zan daina ba duk rintsi duk wuya ina tare da sonki a cikin zuciya ta koda kuwa bana raye. Ga wannan na roqe ki ki kar6i kyauta ta ta farko da na ta6a baki wanda a duk lokacin da ki ka sanya abinda ke ciki zaki kasance cikin farin ciki sbd tamkar kina tare da nine, ina fatar masoyiya ta zata kar6i kyautar da na mata ko don tsalkakekken son da take min,,,cikin tausassar muryar ta mai sa shi natsuwa tace "yaya Anwar ban ta6a kar6ar kyautar ko wane d'a namiji ba face ta mahaifina amma yau zan fara a kanka kuma nayi maka alqawari kai kad'ai ne d'a namijin da zan ci gaba da kar6ar kyautar sa har abada kuwa bazan ta6a sa6a alqawarin da na maka ba, ka riqa tuna hakan ako yaushe domin nima na riqa kiyaye wa" A hankali ya lumshe kyawawan idanun sa yace"InshaAllah Rayyanat bye mu zamu tafi dan Allah ki kula min da kanki " Daga haka ya shiga mota ya zauna seat d'in driver ya tashi mota yana danne hawayen da ke qoqarin zubo mishi yayinda yake kallon fuskar Rayyanat ta jikin mirror. Sarat kuwa bye bye take yiwa Rayyanat yayinda kowannen su ke fitar da hawaye a idon shi . Tsaye take har suka 6ace ma ganin ta nan ta kalli Viva ledar da ke hanun ta ta rungume ta tsam a qirjin ta wasu zafafan hawaye suka gangaro kan kumatun ta inda a hankali ta furta cewa"ina sonka yaya Anwar ba kuma zan daina sonka ba har abada duk rintsi duk wuya ina tare da kai koda kuwa bana raye to kuwa ruhi na zai kasance tare da kai" 🔮🔮🔮🔮🔮 _*Page 2*_ Komawa tayi daga ciki cike da kewar Anwar da Sarat . Bata yarda ta bud'e ledar ba ta ajiye kusa da ledar rogon da Sarat ta kawo mata a cewar sae Mahaifin ta ya dawo ko za a bud'e komai. Har guraren la'asar mahaifin ta bai dawo ba haka taci zama duk yunwar da take fama da ita bata ci rogon ba iya karta ta qara sakawa cikin ta ruwa . Sae guraren qarfe biyar mahaifin ta ya dawo yayinda fuskar shi take cike da damuwa. Rayyanat taje a natse cikin murna tana tarbon mahaifin ta inda ta kai hannu ta d'auke fartanyar da ke kan kafad'ar sa ta kuma d'obo ruwa ta bashi, bai sha ruwan ba sae hannun sa ya tara ya wanke ya zauna a sukwane tare da dafe kan shi. Rayyanat da ko kad'an bata son ganin mahaifin ta cikin damuwa nan take idanun ta suka ciko da qwallah ta durqusa a gaban shi tare da jaye hannayen sa da ya dafe kansa. Muryar ta na rawar kuka tace "me yake faruwa ne Baffa dan Allah ka sanar da ni" A hankali mahaifin ta ya d'ago idanuwan sa da sukayi jajir ya goge en guntayen hawayen da ke gefen su yace"Rayyanat na kasance bani da wani buri a rayuwa sae don ganin na faranta miki hakan yasa tun lokacin da mahaifiyar ki ta rasu ta barki kina jinjira naqi nayi aure don kawai kar ki shiga quncin rayuwa domin bansan matar da zan auro wace iri bace shiyasa na haqura da aure gavad'aya sbd zan iya zamowa auri sake idan har na had'u da matan da ke quntata miki ni kuma bana son kasance wa haka kuma gashi bani da wasu en uwa da zan kaiki a gurin su shiyasa na za6i na raine ki da hannu na,yayinda na zame miki tamkar uwa na kuma so na kasance uban da ba wani abu da zaki nema ki rasa amma talauci bai bar na miki haka ba kiyi haquri Rayyanat da na kasance uban da kullum sae kin nema kin rasa ba yin kaina bane wannan jarabtar ubangiji ce wacce a kullum nake roqon Allah ya kawo muna qarshen ta muna masu lashe jarabawar ba tare da mun sa6a masa ba. Rayyanat nasan ke 'yace ta gari zaki fahimci abinda nake nufi da kuma abinda zan fad'a a yanzu. Rayyanat a yau zamu kwashe komatsan mu mu koma daji da zama can gurin gonar mai gari da nake masa noma....Baffa me yasa zamu koma inda ba kowa ?dole ne Rayyanat sanin kan ki ne wannan gidan ba nawa bane kuma bani da wani gida na kaina haya muke kuma sanin kanki ne duk wata na kanyi qoqarin ganin na biya kud'in haya koda kuwa su kad'ai ne suka rage mana na abinci amma a yau Bala yaje har gurin mai gari yakai qara ta kan cewa bana biyan shi kud'in haya wai har ma yana bina na wata biyu naqi na biya shi, duk da cewa nayi ma mai gari bayanin cewa ba gaskiya ya fad'a ba amma mai gari ya zare kud'in noman da nake binsa na wata d'aya ya bawa Bala na zamo bani da ko sisi kuma Bala ya nemi na bar masa gida wai yana so zai saka wad'an da ke biyan sa duk wata. Ba irin haqurin da ban bashi ba amma yaqi shiyasa mai gari yace idan har zan iya ya bani dama naje can kusa da gonar shi na haqa bukka mu riqa zaman mu a can tunda ba wasu namun dajin da ke cutarwa a gurin. Cikin kuka Rayyanat tace"Allah yasa haka shi yafi Alhairi Baffa"Amin Rayyanat bari naje cikin gari naga ko zan sami wani aikin da zanyi a biyani mu samu abinda muka ci kafin mu kwanta" Kallon mahaifin ta tayi kafin take share hawayen da ke kan fuskar ta tace"Baffa akwai rogo da Sarat ta kawo min ka bari kaci tukun ko zaka fita" Aa Rayyanat ki dai ci in yaso idan Allah yasa nayi nasara sae mu qara cin abinda ya samu,, Baffa rogon fa mai yawa ne kuma tun safe na ajiye shi sae kazo muci tare,,,girgiza kansa yayi yayinda yake qara jin son er shi sbd yasan halin Rayyanat komai qanqantar abu bata yarda taci ita kad'ai sae tare da shi. Nan ya dafa kanta yace"Allah yayi miki albarka Rayyanat ya kuma sanya nasara da albarka a cikin al'amurranki ya kuma sauya miki wannan rayuwa da muke ciki ma'ana nan gaba kad'an ki kasance cikin wadata da walwala had'e jin dad'i mai d'orewa har izuwa qarshen rayuwar ki"Amin Baffa na gode. Nan ta d'auko musu rogo suka ci bayan sun kammala ta d'auko ledar da Anwar ya bata ta bawa Baffan ta ba tare da tace da shi komai ba yace"Rayyanat daga ina wannan ledar ta fito? Cikin jin kunya ta duqar da kanta ta kasa cewa komai wanda hakan yasa nan take ya fahimci inda ledar ta fito yace"Anwar ko sun tafi kenan? Eh sun tafi tun d'azu ,,to Allah ya kiyaye hanya ,,Amin Baffa,,tace"Baffa kayi haquri ban kar6a ba sae don ya had'a ni da Allah"ba komai kuma ai ba a maida hannun kyauta baya. Nan Abban ta yace ta bud'e kayan koda ta bud'e kala biyu ne masu kyau less da atamfa kuma da hijab kala biyu wato kalar kayan sae takalmi taki d'aya da kuma tokar wanka mai had'e da set d'in turare sae wata envelope da aka d'ora akai wacce ta bawa Baffan ta tace shi zai bud'e sbd tana ganin kamar kud'i ne a ciki koda mafahaifin ta ya bud'e en dubu dubu ne sabbi dal har dubu biyar sae wani tsadadden zoben azurfa black an white da wata er guntuwar takarda soke a cikin zoben. kasa had'a ido tayi da Baffan ta yayinda yake miqa mata kayan bata kar6i kud'i ba sae zobe ta kar6a had'e da takarda tace"Baffa ai a gurin ka kud'in ya kamata su kasance da kuma wad'anan tufafin"Rayyanat ki ajiye komai a gurin ki sbd kinga fita zanyi naje naga gurin da ya kamata mu haqa bukka na fara aikin kafin gobe sbd tun da safe yake so mu bar gidan" Baffa muje na taya ka ba musu yace "to adana kayan muje" kwalla taje ta bud'e ta saka kayan suka fita. Da suka fita basu suka dawo ba sae yamma liqis. Da dare Rayyanat bata iya bacci ba sae da ta d'auko wannan takardar ta fara karantawa kamar haka *_"Rayyanat ina so ki saka wannan zoben a yanzu kuma kimin alqawari baza ki ta6a cire shi ba har abada domin cire wannan zoben tamkar kin cire ni a cikin zuciyar ki ne_* Murmushi ne ya bayyana a fuskar ta yayinda take sanya zoben inda ta rufe idon ta a hankali tace" *_yaya Anwar nayi maka alqawari wannan zoben ba zai ta6a fita a yatsa ta ba sae dai idan mutuwa nayi aka cire shi_* Daga haka ta kwanta sae kallon yanda zoben yayi matuqar kyau a yatsan ta take har ta shiga magana a ranta cewa _"Da ace ko mutuwa nayi baza a raba ni da zoben nan ba da nafi kowa farin ciki"_ Yaya Anwar ina ma ace zoben nan mai 6acewa ne da na bashi umarnin ya 6ace a lokacin da na mutu har akaini makwanci na don dai kawai ya kasance ina tare da kai a duk inda nake ko da yake ko ba zoben nan kana tare da ni sbd kana cikin zuciya ta ba kuma zan ta6a iya fitar da kai ba kamar yanda hanta bata iya rabo da jini. Tana maganar ne a fili cikin natsuwa tamkar anwar na kusa da ita. Washe gari tun da asuba ta had'u da mummunan labari su Anwar sunyi had'arin mota kuma ba wanda ya rayu a cikin su kuka taci tamkar ranta zai fita Baffan ta kuwa sae bata baki yake yana aikin rarrashi. Suna cikin haka ne Bala yazo cike da masifa yasa aka yi ta fitar da kayan su ana watsi da su wanda hakan ya qara sa Rayyanat cikin wani yanayi ganin yanda ake wulaqanta mahaifin ta da ke ta ba Bala haquri kan su daina watsar musu da kaya bai saurare shi ba sae da suka fitar da kayan kaf tare da jan hannun Rayyanat suka ingiza ta waje wacce ta kasa yin komai sae kuka . Mahaifin ta ne ya kama ta ta tashi sbd fad'uwar da tayi garin ingiza ta da akayi har ma suka fasa mata baki. Nan suka fara kwasar kayan su suna zubawa a cikin wani tsofon baro da mahaifin ta yayi yayin tallar ruwa a ciki wanda maya biyu sukayi suka gama kwasar kayan na su hakan yasa basu koma cikin gari ba sae qoqarin ganin sun qarasa bukkar da suke su samu su zuba kayan su. Bayan sun kamalla ne mahaifin ta ya zauna yana qara bata baki kan tayi haquri da komai na duniya sae haquri kuma mai wuce wa ne amma Rayyanat tamkar mahaifin ta na qara mata qarfin kuka ne domin da zarar ta kalli zoben da ke kan yatsar ta sae ta sake fashewa da wani sabon kuka . Haka Rayyanat tayi sati tana kukan rashin Anwar da Sarat duk tabi ta rame ta zamo tamkar ba ita ba,sae dai yanzu suna samun d'an abinda suka ci ta hanyar amfani da kud'in da anwar ya bawa Rayyanat. Yau kusan wata biyu kenan da komawar su jeji tun Rayyanat na tsoron zaman jejin har ta saba sae dai har yañzu mutuwar anwar bata sake ta ba bcs duk lokaçin da ta kàlli zoben da ke kan yatsar ta sae ta zubar da qwallah. Tafe suke ita da mahaifin ta sun fito daga cikin gari suna qoqarin tsallake titi nan wata mota tazo a gurguje ba qaqqautawa inda Rayyanat tayi saurin jawo hannun mahafinta don ganin sun kaucewa motar amma tuni motar tayi awon gaba da mahaifinta,a rikice ta d'ora hannu aka ta kurma wani irin ihu mai cike da tsànàñin firgici ganin yanda motar ta sake dawowa kan mahaifin ta tare da jefo bunch d'in 1k kan fuskar mahaifin nata aka kuma ja motar a tsiyace inda duk tashin hankalin da take ciki bai hana ta qure lambar motar da kallo ba wanda bata kauda idon ta ba sae da ta hadda ce numbar. Sannan ta koma kan mahaifin ta da ko shurawa bai yi ba ta shiga girgiza shi cikin kuka tana kiran"kai kad'ai ka rage min Baffa dan Allah ka tashi wlh nayi ma alqawari ko shi waye *BA ZAN BAR SHI BA!*sae na rama abinda ya maka dan Allah Baffa ka tashi kar kace zaka tafi ka bar ni,kasan bani da wani a duniyar nan bayan kai,ka tashi Baffa! Baffah!! Baffah!!! Kuka ta shiga yi sosai har da majina ganin Baffan nata yaqi ya motsa nan ta rungume shi qam a qirjinta tana ci gaba da kuka mai mugun ban tausayi . *_Billy giro😊_* 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:17PM, 1/25/2017] Ummi Ya: 🔮```BAZAN BAR SHI BA!```🔮 ```Na Billy giro😊``` 09/12/2016 🔮```3```🔮 Haka Rayyanat taci gaba da kuka har ta gode Allah dmn ta fahimci tuni Allah ya kar6i ran mahaifinta. Sati d'aya da rasuwar mahaifinta ta baro qauyen su ba tare da kowa ya sani ba. Kuka takeyi sosai a cikin mota har suka iso garin kano ta shiga qarewa garin kallo ba tare da tasan inda zata je ba wani kuka ta shiga yi sosai shike nn yanzu bata da kowa a duniya sae wanda yaga Allah ya taimaka mata,yanzu bata san wace irin rayuwa zata shiga ba kawai dai tasan duk rnr da Allah ya had'a ta da wanda ya kashe mahaifinta Baza ta bar shi ba! koda kuwa itama zata bar duniya ta dalilin hakan. Zaune take kusa da wani gidan mai sae rusar kuka take kamar yanzu ne mahaifin nata ya rasu. Mabaratan da take zaune kusa da su sae kallonta suke abin tausayi dmn ganin suke har sunfi ta dama a yanayin da suka ganta ciki. Ta jima sosai a gurin ga yunwa ga qishi ta tashi tsaye da qyar sbd jirin da ke d'ibar ta, kallon mabaratan da ke kusa da ita take ta hango er gorar ruwa aje kusa dasu ta fara tako cike da son taje tace su en mata ruwan tasha ba tare da ta damu da ganin su mabarata bane ita dai ta samu ta kawadda qishin da take ji. Gab take da isa gurin su wata irin tsaleliyar mota ta tsaya a gurin wanda ke ciki ya sauke glass d'in motar a hankali yana kallon mabaratan cikin wani yanayi na qyama kamar wanda zai yi amai. Hannu yasa ya zaro kud'i a aljihun sa 1k bunch ya jefa musu kud'in dai dai Rayyanat ta juyo kan ganin yanda taga mabaratan sun qure guri d'aya da kallo, yanayin yanda ya jefa musu kud'in yasa gabanta yayi mugun fad'uwa kuma tabbas kalar motar da ta kad'e mahaifinta ce take gani tsaye a gabanta Mabaratan sukayi ruu! dmn d'aukar kud'in da aka jefo musu sae qoqarin kada Rayyanat suke da kud'in ke tsakiyar qafafunta ita kuwa ko qwaqqwaran motsi ta kasa sae qarewa motar kallo take ba tare da ta iya hango wanda ke ciki ba dmn tuni ya mayarda glass d'in motar sa ya rufe. Tako ta fara a hnkli dmn ta kai idonta ga numbar motar,taga ba ko shakka ita ce numbar motar da ta kad'e mahaifinta wani irin yanayi Rayyanat ta tsinci kanta a ciki marar misaltuwa idanuwanta suka ciko tap da qwalla ta samu da qyar ta d'aga yatsarta tana nuna numbar motar, cikin rasa iya motsa koina na ga66an jikinta take ci gaba da kallon numbar. firgigit tayi ganin motar ta fara tafiya sauri sauri ta shiga bin motar wacce still yatsarta na kan numbar motar tana nunawa........"ke! ke!! ke!!!" shine abinda mutanen gurin keta fad'a amma sam hanklin Rayyanat na tare da motar hakan yasa taji an kwashe ta kai tsaye kanta ya daki wani guri tun daga lokacin bata qara sanin inda take ba. Matar da ta kad'e Rayyanat ce keta faman zarya a asibiti cike da takaici se faman duba wristwatch d'inda ke hannunta take....wayar ta ce ta shiga ringing ta d'aga cikin sauri tace"yauwa honey pls kazo *MAN HOSPITAL* na kad'e wata yarinya ne" daga haka ta katse wayar ba jimawa ya iso sae ga doctor ya fito yace taje yanzun zata iya ganin yarinyar. Sosai Rayyanat ta samu rauni har dai saman goshinta sae dai bata farfad'o ba sae bacci take ana mata qarin jini. "Garin yaya haka ta faru?cewa da mijinta Tace "Honey kasan matsalar talaka da baqin hassada duk inda motar mai kud'i ta wuce sun fara binta da ido kenan shine fa ita bata tsaya a kallo ba har bin motar take kamar motar ubanta! sae wani qoqarin kamo motar take ana faman kiranta amma a banza! gashi yanzu duk ta 6ata min tsari har yaya ya tafi ya barni may be ma har jirgin su umma ya sauka ya kai su gida,eyya sorry yanzu ki tafi kawai in yaso ni na tsaya. Tunda Rayyanat ta farfad'o bata da aiki sae na kuka duk yanda yaso tayi mai magana taqi har kusan kwana biyu snn aka sallameta . Gidan shi yaje da ita suna shiga falo yaji qarar fashewar glass da sauri ya kalli inda yaji sautin yaga matar sa ce ta saki glass cup tana masa wani mugun kallo cikin tsananin kishi . Da mamaki yace"lafiya pretty"har ka tambaya! wnn wace er iskar ce ka shigo min da ita a gida! Yace"ikon Allah yarinyar da ki kad'e ce fa aka sallame ta yau......to dan ita ce sae ka wani kwasota ka kawo min ita a gida har da wani riqo mata qunshin ledar ta,to pretty ina kike son taje bata qarasa jin sauqi ba kuma kinsan har yanzu ko magana batayi ba bare asan daga inda ta fito....fuuu! tazo ta fizge qunshin Rayyanat dake hannun shi tace"Ai tunda ba gidan ubanta bane wlh sae ta fita!da gani ma irin shegun yaran nn ne da iyayen su ke jefarwa suna gantali a hanya shine tayi shiru taqi fad'in inda ta fito ita ala dole taga ta samu mafaka,nn ta jefa ma Rayyanat qunshinta tace"oya! fitar mana daga gida shegiya! kije can ki qarata da baqin gantalin ki da uwar ki taja miki! A hnkli Rayyanat ta duqa ta tsince en kayanta da suka fito cikin ledarta snn ta tashi tana mai share qwallah a idonta ta fita. ```Billy giro😊``` 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:18PM, 1/25/2017] Ummi Ya: 🔮```BAZAN BAR SHI BA!```🔮 ```Na Billy giro😊``` 11/12/2016 🔮```4```🔮 Cikin hanzari mijin pretty yabi Rayyanat yana fad'in ta dakata. Kamar kar ta tsaya sae kuma ta tsaya ba tare da ta juyo ba sbd kuka take yi sosai har yana so yaci qarfinta. Kafin ya qarasa gurinta pretty tayi sauri tasha gabanshi tace"wlh bafa zata zauna a gidan nn ba!bai kula ta ba sae qoqarin wucewa yake tana tare mai hanya ya tsaya tare da nuna ta da yatsa snn yace"kinga pretty kar ki kaini qul fa! daga haka ya ra6a ta gefenta ya wuce yace da Rayyanat "muje"ta sake shan gabanshi tace"ban gane kuje ba ina zaka tafi da ita? Koma ina ne ba ruwanki yanzu,tunda ke baki san ki tasauya ma bayin Allah ba!ta wani le6ace baki tace"meye abin tausayi wa talaka ko talaka mabaraciya wad'anda basu da burin da ya wuce ganin bayan dukiyar mutum kullum cikin roqo da fad'in a basu,basa nema sae dai a nema a basu sbd baqin lalaci irin nasu. Ki iya bakin ki pretty kullum cikin aibata talaka kike talaka ba abin gori bane dmn kema baki wuce Allah ya jarrabace ki da talauci ba........ Tuf!bakin ka ya sari d'anyen kashi wlh ni Allah tsare ni da baqin bakin ka! Ganin abin na son zama musu fad'a Rayyanat tace"ka bar shi kawai nagode ni zan tafi koma ina ne" Yace"Kwantar da hnklin ki ba nn gidan zaki zauna ba gidan kakata zan tafi dake har ki qarasa jin sauqi tukun....cabd'i!lallai ma Nasir kai baka ji me tace bane "wai zata tafi koma ina ne" hakan fa na nuna ba tada asali amma shine har kake qoqarin kaita gidan kaka! Wai pretty me yake damunki ne ya zaki kama fad'ar magana akan abinda baki da tabbacin sa! Murgud'a mai baki tayi tace"wane tabbacin kuma zan nema bayan sanin kanka ne duk er asali bazata kama gantali kan hanya ba har ma tana fad'in koma ina ne zata tafi ai duk d'an asali ba zai ce haka ba sae dai yace zai koma gurin en uwansa! Guntun tsaki yayi snn ya kalli Rayyanat yace"baiwar Allah gaya min sunanki" Sae da ta share hawayen da keta faman sintiri a kan fuskarta snn tace"sunana Rayyanat..... Mtsw kaji wani kilinbibi d'an qauye ne yasan ya qawata suna haka ai sae dai Rayyanatu hm!wai Rayyanat....yi mana shiru a nn pretty meye ruwanki da sunanta kuma! yace"Rayyanat yi haquri sanar dani abinda ya kawo ki garin nn dmn na fahmici kamar ke ba er garin nn bace ko"kuka kawai Rayyanat ta fashe dashi ,Nasir yayi shiru yana nazari inda ya fahimci tabbas akwai abinda ya faru da Rayynat wanda bata son a tambaye ta inda ta fito tunda ko asibiti haka take ajiye mai kuka idan ya tambayeta nn ya tsara a ransa bazai qara mata tambayar ba har se taji sauqi tukun. Yace"daina kuka zo muje" pretty tayi saurin riqo hannun shi tace"honey bafa inda zaka je da ita"wani mugun kallo ya watsa mata ya kuma fizge hannun shi,cikin tsiwa tace"ai ko wlh sae dai ka za6a ni ko ita! don duk ka fita da ita nima sae nasa qafa na bar gidan nn na tafi gidan mu"yace"in kin iya kivar duniya gabad'aya ba ma gidan ba! Daga haka yasa qafa ya fita shida Rayyanat. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:18PM, 1/25/2017] Ummi Ya: 🔮```BAZAN BAR SHI BA```🔮 ```Na Billy giro😊``` 11/12/2016 🔮```5```🔮 Suna shiga gidan kakar ta tarbe su da murna kamar har Rayyanat d'in ta sani dmn akwai ta da son mutane sosai. Bayan sun zauna ta kawo musu ruwa snn ita ma ta zauna suka qara gaisawa tace"daga ina haka muka samo baquwa nasir?, Nasir yace "wlh kaka pretty ce ta kad'e ta a bisa qaddara shine bayan ta kaita asibiti da kwana biyu aka sallamota to har yanzu dai bata fad'i ita wace ce ba dmn duk na tambayeta sae tayi tamin kuka , kawai dai ta sanar dani sunanta Rayyanat ,naso ta zauna can gidana har ta qarasa jin sauqi amma kinsan halin pretty shine naga kawai na kawota gurinki dmn zata ma fi jin dad'in zama a nn. Kakar da ta bude baki tun fara mgnr sa tace "ikon Allah, wani irin tuki take har xata buge yar mutane snn kuma ta ki Bari ta xauna gidanta har ta warke, ni dae yaran Kabiru suna bn mmki da irin halinsu" Nasir dae yyi shiru bae ce komae ba, ganin sae fada kaka ke tayi kmr xata ari baki yasa yace "ynxu dae kaka kiyi hkuri hka, sae ta xauna gun ki har Allah ya sa a samo yan uwanta" kaka tace "yo in bata xauna nn ba ina xata xauna da" Nasir yyi murmushi yace "gskya ne kaka" Rayyanat kam sae kallon tsohuwar take nn da nn taji ta kwanta mata taji kuma xata iya xama da ita. Kakar ta tashi ta shiga kitchen ta d'ebo abinci ta kawo mata tace "ki saki jinkinki fa ki d'auka nan tamkar gidan ku ne kinji, ita kuma xata xo ta sameni har gida, tukin ma daga ynxu sa xanyi Khabiru ya hanata tunda abun nata har da buge mutum, kwanaki ma hka ta buge dan mutane" Nasir dae bae ce komae ba, Rayyant ta sunkuyar da kanta tana mai share qwallah had'e da ajiye d'an ledar da ke hannunta. Kakar tace "kawo ledar na shigar miki da ita idan kin kammala sae ki watsa ruwa ko kyaji d'an damar jikin ki, ki kwanta ki huta" Bayan takai ledar ta dawo tana mai duban Nasir tace"ina ce ka siya mata magungunan da zata ci gaba da sha? Nasir yace Eh akwai magunguna a cikin ledar ta idan ta gama cin abinci sae tasha kafin tayi wanka dmn lokacin shan magunan ma yayi. Yana gama fad'ar haka ya tashi yace"inna ni zan tafi sae anjima idan na dawo " inna ta washe baki tace "To Allah yyi maka albarka" ya amsa da Ameen yana murmushi ya nufi kofa xae fita, juyowa yyi yace "am yau man bai shigo bane inna? Inna tace " waye kuma hka?" Nasir yyi dariya yace "Mai gidan ki mana" ta tabe baki tace "Tun da safe ya shigo da dan rashin mutun cin sa, amma na taka masa burki, to har ynxu dae bn gansa ba" Nasir yyi dariya yace "to shknn" inna tace"ko da wani abu ne?" Aa ba komae naga ko yaushe na xo yana nane da ke ne," Har gurin motar sa ta rakashi ta dube shi da kulawa tace"Nasir gaskiya yarinyar nn da akwai alamomi ban tausayi a tare da ita jifa tunda kuka shigo bata da aiki sae na share qwallah,ai ma inna kad'an kika gani baran idan aka tambayeta inda ta fito, shiyasa yanzu nafi son sae taji sauqi tukun ko zan sake tuntu6ar ta. To Allah yasa ta kirki ce kamar yanda nake ji a raina ni dae ta kwanta min wllh, Nasir yace Amin inna. Daga haka ya shiga motorsa ya wuce, inna kuwa ta koma daga ciki. Nasir kuwa yana zuwa gida ya samu gidan a hargitse duk pretty ta farfashe abubuwa ta kuma tafiyarta gidan su kamar yanda tace. 6angaren pretty sae kuka take sosai a jikin wata mata da nake sa ran ummanta ce ita kuwa sae masifa take inda take fita ba nn take shiga ba na ganin har dare Nasir yaqi zuwa ya sasanta shida pretty. Wani gaye ne ya shigo d'akin Alhmdlh ya had'u ta koina baya da makusa tamkar balarabe fari tas dashi,yana d'auke da d'an siririn saje kan fuskarsa . D'ayan hannunsa yana riqe da suit baqa kalar wandon da ke jikin sa,yayinda rgr jikinsa ta kasance fara mai ratsin layi layi. D'ayan hannunsa kuma yana sanye a cikin aljhun wandonsa. tsaye kawai yayi yana kallon su ba shi da niyyar cewa komai . Mamar ce ta fara ganin shi ,ya gaishe ta ta amsa inda cikin nuna damuwa sosai tace"man kaji abinda Nasir yayi wa qanwar ka pretty. Nan mamar ta zayyana mai abinda pretty ta fad'a mata. Bai ce da mamar komai ba ya kalli kanwar tasa fuskar sa ba yabo ba fallasa yace "garin ya akayi kika kad'e ta? Kmr xata yi kuka tace yaya ina lokacinda zamu tarbo su umma har ka tsaya wani gidan mai ka bada sadaka? Yyi shiru yana kallonta, hkn yasa ta turo baki tace yaya ni fa ba laifi na bne yarinyar ce Jaka, ina ga daga kauye ta fito, wani mugun kallo ya shiga yi mata, ta dauke kai tana murguda baki, ya gyada kai yace "daga yau kar ki kuskura ki kara jan mota" ta xaro ido tana kallonsa tace "sbda me, ko mijina fa bae hanani va yaya" tsawa ya daka mata yace "nace kar ki kuma jan mota" Daga haka ya fita ba tare da ya tsaya jin me zata ce ba . Tafiya yake a hnkli har ya isa 6anfarensa. D'akin sa wani irin d'aki ne mai masifar kyau da tsari komai fari tas sae qawar da akayi da golden ga tsarin d'akin ba wani tarkace kamar tsarin d'akin turawa. Frigde ya bud'e ya ciro gorar ruwa ya bud'e ya tsiyaya ruwan a glass cup yasha snn yaje ya cire kayan jikin sa ya sanya white bathrobe ya nufi bathroom. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:18PM, 1/25/2017] Ummi Ya: 🔮```BAZAN BARSHI BA```🔮 ```Na Billy giro😊``` 11/12/2016 🔮```6```🔮 Ya jima sosai kafin yake fitowa yana gama shiri yaji ana masa knocking yaje ya bud'e qofa idanunsà suka sauka kan qanwar sa pretty dake tsaye riqe da trayn abinci fuskar ta fam kamar zata fashe don fushi tace"amma dai yaya zancen na daina tuqi da wasa kake min ko?mugun kallo ya watsa mata ya juyarwarsa ya koma daga ciki,ta shiga ta ajiye trayn sea qunquni take ita ba wanda ya isa ya hanata tuqin mota kan wata jaka can er qauye marar asali ma, Bai kulata ba har ta qaraci surutunta ta fita. Washe gari sallah kawai tayi tace da ummarta"ni xan koma" Umma ta saki baki tana kallonta snn tace"amma pretty ni nasara ke wace irin mace ce wlh kowace mace na ganin ta samarwa kanta enci amma banda ke ,wane irin abu ne da baza ki bari sae nasir yazo da kansa ba ko zaki koma ,wlh kwata kwata kin 6ata kanki da sonda kike yiwa nasir kmr ba nice na haife ki ba....nifa umma ba haka bane naji kina waya da Abba yana kan hanya shiyasa zan tafi kar yazo ya sameni ya min fad'a kuma kinsan jiya da dare nasir yazo har yayi ta kiran wayata naqi na d'aga,to shi baqon gidan nn ne da bazai shigo ba sae ke zaki fita ki same shi ai inace yaje 6angaren uwar sa amma yaqi zowa nn,ai umma barshi don ni bama gidan sa nayi ba wlh gidan inna zan tafi,to idan inna ta tambayeki lafiya fa? Ai inna ce zan kwashe da ita dai dai ba kamar Abba ba ,to ai sae ki tashi kiyi niyya dmn gab yake da isowa garin nn. Sauri sauri taje tayi wanka ta shirya sae neman makullin motar ta take duk ta jigata kamar zata yi kuka ta kalli ummarta da ta shigo tace"umma ina makullin mota ta? Yayanki yazo ya kar6a....haba umma meyasa kika bashi, kije ki roqe sa mana ai zai baki ,Allah umma kinsan da kamar wuya kidai roqa min shi ya bani, Aa ba ruwana can tsakanin ku ne kije ki gwada sa'ar ki idan ya baki to. Wani abu yace miki da zai kar6i makullin motar ne?ba abinda yace min kawai dai ya kar6a ya tafi. Cikin 6acin rai ta fito tayi kici6is da yayanta da kuma mijinta Nasir a nn harabar gidan kallo d'aya tayiwa Nasir ta kauda kai ta kalli yayanta tare da marairiace fuska tana roqon ya bata makullin motar ta,kallon nasir yayi yace"sae kaja matar taka ku tafi" Ya sa qafa zai wuce tayi saurin shan gabanshi tace"pls yaya kayi haquri ka bani" tsawa ya daka mata yace"wai ina wasa dake ne da kike tunanin zan kar6e abu na baki! Le6ace baki tayi zuwa kuka tace"yaya ba fa laifi na bane na gaya ma" Wayar sa da tayi ringing ya d'aga ya bar gurin ,kuka ta fashe dashi nasir yazo yaja hannunta ta fizge hannun taje ta shiga mota shima ya zagaya ya shiga yaja motar tana ganin ya hau titin zuwa gidan su ta dalla mai harara tace"nifa ba gidan ka zan tafi ba don ka sani gidan inna zanje gara tun wuri ka sauya hanya don ko munje gida ba shiga zanyi ba wlh ,kuma sae naci uban wnn er iskar yarinyar da ka kaiwa inna wacce a dalilinta aka hana ni jan mota sae naga ta yanda ma zata zauna gidan inna d'in dole ta barshi tunda ba gidan kakarta bane ko wani nata. Nasir yayi shiru yana kallon pretty shidai ko kad'an baya son masifar nn tata gashi aikin kenan idan aka ta6o ta. Hannun ta ya riqo tare da kai mata sumba snn yace"da kika yi shiru sae kika min kyau kamar ace ko yaushe haka kike ba ruwanki da fad'a" Hm ba wani dad'in baki da zaka min nifa sae ka kaini gidan inna ,kallon ta yayi yana tunanin wayon da zai mata dmn yasan duk taje gidan inna ba qaramar rigima za'ayi ba,yace"gidan inna kwantar da hankalinki zan kaiki amma sae kin raka ni gida nayi wanka tukun,ta6e baki tayi tana kallonshi snn tace"wankan me zakayi da baza ka kaini gidan inna ba har sae na raka ka,banyi wanka ba da safen nn ina gama sallar asuba naje gida dmn nazo dake, kuma yunwa nake ji sosai kinsan kin tafi kin bar ni ba abinci kuma yau da safe ma haka,shine nake son ki had'a min breakfast kafin na fito wanka kinji, ya fad'i haka ne cikin marairaicewa had'e da tsare ta da ido dmn yasan da ya mata haka bata iya masa gardama, ta kauda fuskarta gefe kamar baza ta amince ba sae kuma tace "naji" Karfe takwas da minti goma na dare Rayyanat na kitchen tana yi ma inna goge goge bayan ta gama wanke kwanukan da suka ci abincin ta ji an bude katon gate din gidan alamar mota xae shigo knn, duk lkcn da taji karan bude gate din sae gabanta ya fadi don ba sabawa tayi ba, bayan kusan minti bakwae inna ta shigo kitchen din ta gwalo ido tace "lahh bar maki aikin Hurera tayi" Rayyanat tace "A'a ni na karba inna" inna ta washe baki tace "ayyo!sannu da aiki jikata, ynxu duk ke kika gyara kitchen din nn hka" Rayyanat tayi murmushi ta sunkuyar da kanta bata dae ce komae ba, inna tace "to miko min wancan kulan abincin in kai ma mai gidana ya xo" Rayyanat ta dauko ta mika mata da ladabi inna ta fita tana cewa "yau ko dan kankanan da lemo bae siyo min ba ya kwaso kafafuwa ya xo xae cinye min abinci uwa shi ke siyo min" bayan minti goma da fitan inna Rayyanat ta gama abinda take a kitchen din baka taba cewa daga kauye take komae nata tsaf tsaf take yi, da kyar ta iya fitowa daga kitchen din a sanyaye tuno babanta da ta yi, hkn yasa kwalla ya cika idonta, tayi saurin sharewa bata tarda kowa falon ba sae hurera yar dattijuwar matar da ke goge tiles din falon ta kalleta tana murmushi tace "sannu Rayyanah, ki tafi can daya falon inna na can, amma ga furar ta nn da na dama mata ki dauka ki tafi mata da shi, Rayyanat ta gyada mata kai kawae ta dauki furan da ke rufe kan centre table ta nufi falon da Baaba Hurera ke nuna mata, inna na xaune kan tabarma ta tankwashe kafa ta kapa ma tv ido tana kallo uwa tasan abinda ake yi, shi kam yana xaune kan three seater rike da remote waya na kare kunnansa alamar waya yake, kallonsa kawae Rayyanat take a sace kuma a tsorace sae dae har lkcn bae juyo ba, inna ta juya da sauri ganinta a tsaye tace " A'a karaso mana Rayyanah" Sae a snn ya juya yana kallon da warce kakar tasa ke mgna, Rayyanat ta sake kwanon furar hannunta ba tare da ta shirya ba, inna ta mike da sauri tana salati, ya katse kiran da yake shi ma ya mike yana yatsine fuska yace "ina kika samo mai aikin nn kuma Inna, idan xa ku dauki masu aiki ku dinga bincike da kyau don Allah ku dena dauko yara irin hka masu kananan kwakwalwa, bnda hka meye xata shigo falon mutane ta sake masu kwanon fura a kasa kmr wata me tabin hnkli" juyawa Rayyanat tayi da gudu ta fice daga falon a rude. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:18PM, 1/25/2017] Ummi Ya: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 ```Na Billy giro😊``` 16/12/2016 🔮```7```🔮 Oh Allah yoni hajara!kai muhammadu ai wnn yarinyar iyakar hnkli da natsuwa tsautsayi ne kawai da in yazo ba mai tare shi. Inna ina hnkli a nn da shigowarta ta 6arar da fura kmr wacce bata saba ganin mutane ba,kudai 'ya'yan kabiru haka kuke abu kad'an ya isheku masifa, inna yau maigidan naki kike gaya ma haka, yo ai ko waye kai tunda ka ta6a er albarkar nn dole na maka magana yarinya tsakanin jiya iyau lafiya muke zaune sae gashi kazo zama d'aya ka rikita ta har ta tafi da kuka,nidai inna da wnn mitar kira hurera tazo ta goge gurin nn ,kuma dan Allah kidaina kwaso iren iren yaran nn sam ba abin yarda bane da har kike saurin bama yarda zama d'aya,wai er had'uwar jiya zuwa yau ce kike kora min bayani kamar kun shekara, masifa inna ta shiga yi dashi,Man ya bita da kallo yana murmushi har ta fita. Taje ta samu Rayyanat a d'aki sae kuka take rusawa, tayi zaune tana rarrashinta har ta samu tayi shiru. Rayyanat ta tashi tana share hawaye tace"inna bari naje na kwashe furar"a'a ai nasa hurera ta kwashe, kika sata inna nifa na 6arar,kar ki damu indai hurera ce bata da wnn,bari na tashi naje nabar maigidana shi kad'ai ,tace"to inna"inna na fita Rayyanat ta kifa kai taci gaba da kukanta. Da dare Nasir yazo ya samu sun kammala cin abinci sunyi zaune suna kallo ya gaida inna snn ya samu guri ya zauna ,Rayyanat ta sadda kanta qasa tana miqa gaisuwa ya amsa gaisuwar snn yace"ya jiki ?tace"Alhmdlh yace"kina dai shan maganin ki akan lokaci ko? Gyd'a masa kai kawai tayi tana wasa da en yatsunta. Ya maida dubansa gun inna da ta miqe qafafu tana kallon Indian film kamar wacce kejin wani abu dmn duk ta tattara natsuwarta a can. Sae da abin ya bashi dariya sae dai bai yarda yayi ba dmn yasan masifa zata aje mai in tasan dalili dryr dmn kallo d'an gidan ta ne ba mai shiga tsakanin su. Yace"inna hln mai gidan naki ya koya miki indiyan ci ne naga kin maida hankali sae sauraren su kike?yo ina fa na iya Rayyanah na saka ma shine nayi zaune nima ina kallon abin tausayi naga sae wulaqanci yarinyar kesha a gun mijinta,dariya yayi yace"to ke inna ya akayi kika san mijinta ne? Yo kai Nasir banda idanu ne ko ko banda fahimta,gashi har gado d'aya naga suna kwanciya ai wnn sae miji da mata,dariya kawai yayi ya ajiye zancen dmn ya kalli film d'in ba miji da mata bane budurwa ce da saurayi ya mata ciki shine yake wulaqanta ta. Hannu yakai ya shafi sumar kanshi yace"inna zan tafi "ah ah kaiko da wuri haka ,inna aski zanje sae dai gobe idan na sake shigowa ,to Allah kiyaye , sae da yace"Amin snn ya fita. Ko minti ashirin bai yi da fita ba sae ga Man ya shigo gidan sae dai shi ba kallo ya samu suna yi ba tausa ya samu Rayyanat tana yima inna. Rayyanat na ganin shi sae duk ta nemi natsuwar ta ta rasa, haka ta dake ta gaida shi ta kuma yi saurin tashi tabar gurin. Bai ma amsa gaisuwar ba sae inna ya gaida ya ajiye ledar da ya shigo da ita kusa da inna snn ya zauna,inna ta tashi zaune tana washe haqora tace"me kuma kazo min dashi yau? Sae da ya jingina bayansa kan 2 seater d'inda yake zaune snn yace"gasasshiyar hantar rago ce na siyo miki kan hanya" Kai Allah dai shi yi maka albarka kamar kasan nayi kewarta wlh,ai inna har fruit naso siya miki se na manta,,ayyo ai d'azun da rana Nasir ya shigo min dasu munsha har mun gode Allah har ga saura a fridge ko na d'auko ma zaka sha?Aa inna, to abinci kam zaka ci dai ko? shima haka dmn a qoshe nake, yau tawaye kamin kenan ,Aa naci abinci ne a gidan wani abokin mu da yayi sabon aure muka je, oh ni kakata talatu kai yanzu ka gwammace kayi ta zuwa gidan abokanai ba a zuwa naka , wai nikam yaushe zaka fara ra'ayin aure ne muhamnadu,hm inna ai aure lokaci ne dashi kin sani in lokaci yayi zanyi har ma a wayi gari watarana kina zaune zagaye da en jikokin ki, nn inna ta washe baki tace"Allah nuna mana lokaci muna masu rai da lafiya"Amin inna. Washe gari Rayyanat ta gama taya hurera duk ayukkan da take tazo tayi kwance qasan tiles tana jiran fitowar inna daga gurin wanka nn bacci yayi awon gaba da ita. Pretty ce ta shigo gidan tayi tsaye tana kallon Rayyanat dake bacci tace"yau zaki ci ubanki yarinya" Nan taje ta bud'e fridge har ta d'auko gorar ruwan sanyi sae kuma ta girgiza kai ta mayar ta nufi kici tana murmushin mugunta ta d'auko flask d'in ruwan zafi tazo kai tsaye ta bud'e tana kwara ma Rayyanat su a jiki , ihu Rayyanat ta saki ta tashi a firgice tana lalubar bayanta inda taji saukar ruwan zafi. Mari pretty takai mata tace"er iska ai yau sae kin bar gidan nn wlh tunda bana ubanki bane! Taja Rayyanat kamar wata kayan banza ta ingizata waje da qarfi sae kawai Rayyanat taji ta fad'a jikin mutum hkn yasa taji saukar wani irin gigitaccen marinda ya soma fitar da ita hayyacinta. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:18PM, 1/25/2017] Ummi Ya: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 ```Na Billy giro😊``` 17/12/2016 🔮```8```🔮 La'ilaha ilallahu Muhammadu rasulillahi sallallahu Alaihi wa sallam! Cewar inna wacce ta fito daga gurin wanka tace"Muhammad me rayyanah ta muku ne da zaku mata taron dangi tun ina bayi naji ihunta Fatima na faman sirfa mata masifa yanzu gashi na samu ka tafka mata uban mari haka!inna ta qarasa magana cikin muryar kuka irin na tsafi d'in nan. Nan take man damuwar sa ta bayyana ya shiga bawa inna haquri bata kula shi ba sae kuka take taja Rayyanat suka koma cikin d'aki. Pretty ta kalli man dake qoqarin bin su inna tace"to wai meye abun damuwa kabar su mana tunda kasan halin inna dama saurin kuka ne da ita in ba don shi ba meye abin kuka wa wannan er qauyen,harara ya dalla mata yace ai duk ta dalilin kine banga uban me ya kawo ki gidan nn ba....kamar ya yaya...zan mare ki wlh idan baki 6ace min da gani ba! Turo baki tayi tana faman gunguni har ta fita gidan. Man kuwa shiga d'akin yayi amma a iya falo ya tsaya inna ta fito tana shar6ar hawaye zata d'auki wayarta dake kan TV stand yace"inna yi haquri Allah sam na d'auka rashin hnklinta ne yasa ta fad'o min a jiki ban san cewa pretty ce ta ingixo ta ba,amma Muhammadu ai ka saurara mata ko! yanzu gashi bayan fasa mata baki da kayi duk bayanta ya kwaye... Kamar ya inna nifa marinta kawai nayi... Yo kai ba kasan ruwan zafi pretty ta watsa mata a baya ba,shiga ka duba ta kaga ai nasan dole sae an yanke wnn ftr ,ta qarasa maganar cikin kuka snn tace"ka shiga mana ka duba min yarinyar mutane kazo kayi tsaye se kallona kake! Ba musu ya shiga ya sami Rayyanat ruf da ciki se kuka take abin tausayi zip d'in rigar ta a bud'e fatar bayanta har yyi ja, kauda fuskar sa yayi tare da sauke ajiyar zuciya snn ya kalli inna dake tsaye kusa dashi tana matsar kwalla yace "inna ina ganin ta sosa bayanta ne a lokacin da aka watsa mata ruwan, kuma wnn da gani ma ba wani ruwa me xafi bne, Rayyanat da bata ji shigowarsa dakin ba sae maganar sa taji tayi saurin tashi xata rufe zip d'in rgrta, inna ta karaso da sauri tace "A'a Rayyanah kar ki rufe ai shi likita ne zai duba miki bayanki in kuma baxae iya ba sae ya kira mana ubansa ya xo ya kai mu asibiti," Rayyanat ta girgiza kai ba tare da ta kallesu ba alamar bata so, inna tace "A'a ki yi haquri ya duba ki kinji jikata" Man da takaici ya ishe shi yace "inna bari kawai zan turo a duba ta" yana kai wa nn ya fice daga dakin kmr xae tashi sama. Sae da ya kira wani abokinsa likita snn ya bar gidan ya nufi gidan kanwarsa pretty. Yana isa gidan Nasir ya samu kan dining sama sama suka gaisa yace masa "ina pretty" kafin ya basa amsa sae ga prettyn ta sauko, bata damu da ganin fuskar yayanta ba annuri ba ta daure fuska ssae tace "gani yaya lafiya dai ko" Yyi mata wani mugun kallo yace "me wnn yarinyar ta miki da zaki xuba mata ruwan xafi a jiki," shiru pretty tayi tana kallon shi kamar bata san me ya faru ba har lkcn fuskarta a tamke, ya daka mata tsawa yace "ya kika min shiru kina kallona ina maki mgna?" Ta tabe baki tace "To nifa yaya ban gane zancen da kake ba bare na iya ce maka wani abu," nn ya fahimci ta fita ne bada ixinin nasir ba shine take wani nuna kamar bata san da zancen ba. mari ya kai mata don bata da nisa daga inda yake yace "yanzu kin fahimci zancen nawa!ko kuma sae na qara miki wani," da sauri taja baya tana kuka don ganin da gaske yake, tace "to shine zaka wani mareni wlh sae na gaya ma umma! daga haka ta tafi da gudu tana kuka ta haura sama. Duk da Man ya fahimci Nasir yana buqatar jin bayani bai tsaya yi masa ba ya tafiyar sa hakan yasa nasir ya tafi ya haura sama gun matarsa da shima ya fahimci gidan inna taje bai sani ba. Da shigarsa ta taso ta rungume shi tana kuka tace "ka gani dai ko honey ban masa komai ba yazo ya mareni," mugun kallo yyi mata yace "bana son qarya pretty nasan halin Man ba zai zo haka kawai ya mareki ba ,ba makawa gidan inna kika je gun Rayyanat kika aiwatar da nufinki ko?" shiru tayi alamar can taje d'in, nn ya shiga yi mata fad'a sosai daga qarshe yace duk ta qara fita bada izinin sa ba sae ya sanar da Abbanta, fushi ta shiga yi dashi bai kula ta ba ya tafiyarsa yaci abinci ya fice daga gidan. Gidan inna ya nufa yaje yaga aikin da pretty tayiwa Rayyanat lokacin ma har likita ya xo ya dubata, bata wani kone ba sae dae fatar jikinta da yyi ja ssae. Sosai ya bata haquri daga ita har inna da abun yabi ya dama har tana cewa a kira mata kabiru, Nasir dae ya dinga bata haquri yace shi zai yi maganin abun amma fafau inna tace ita fa sae taje shima zai kaita gidan da kanshi. Haka ko akayi dmn tare suka fita shida inna suka bar Rayyanat ita da hurera. Wani makeken gida suka nufa kyace gidan shugaban qasa ne kan tsari da kyawo irin nashi, kuma ba wani gida bane face gidan su Nasir d'in da kuma su pretty wato qanwar man sbd gabad'ayan su family's ne en wa da qani ne, Baban su Man shine babba snn mahaifin Nasir bayan shi kuma akwai wani Alhj sa'eed wato qanin mahaifin Nasir inda shi kuma yana da qanwa mai aure a garin kd dukkan su 'yayan inna ne shine maxan suka had'e kansu suna zama gida d'aya sae dai kowa da nasa 6angare. Suna shiga gidan inna ta nufi 6angaren su pretty sae ga wata yarinya tazo da murna ta tarbe ta tana fad'in "he inna nida nake batun zuwa gurinki shine kika zo, inna ta washe baki tace "tukuna saukar yaushe Ameera? Yau yau d'in nan aka bamu hutu inna ,to ina er uwar taki saliha? "Tana 6angaren su tare ma ne zamu tafi gurin ki nasan yanzu haka ta shirya tana can tana jirana wlh, inna tace "ayyo to ai yanzu komawa zanyi sae mu tafi tare je kira min Abbanku kabiru yazo ina da magana dashi, tace "to inna zauna na kira miki shi"inna ta zauna ita kuma ta haura sama. Nasir kuwa wani 6angaren ya nufa da alama shine na iyayensa dmn matar da ya samu zaune a falo sak suke kama dashi, cike da ladabi yaje ya durqusa ya gaisheta yana qoqarin tashi yaji an rungume shi ana fad'in "oyoyo yaya" cike da murmushi yake kallon wacce ta rungume shi yace "A'a saliha shin yau ne hutun ku ko to wa ya d'auko ku? turo baki tayi snn tace "Abba ne yaje da kanshi tunda kai kaqi zuwa "oh no saliha yi haquri sam na manta da yau ne hutunku amma umma ya akayi ba a sanar dani ba sae Abba ne yaje da kanshi? Mamar tace "Abban ne yace akwai aikinda yasa ka shine ya tafi dakanshi ya d'auko su, Nasir yace "eh gaskiya ya bani aiki tun jiya ban samu na qarasa ba amma inshaAllah yanzu zanje office na kammala kafin ya tambaye ni, nn ya kalli saliha yace "ina zuwa haka naga kinci kwalliya? Tace "Gidan inna zamuje nida Ameera," eyyah ai tare muka zo nida inna tana ma 6angaren su Ameera, Saliha ta 6ata fuska tace "ita ko dai inna...ai ba jimawa zatayi ba dn inaga sae na maida ita gida ne ko zan tafi office ,yauwa bara naje na ganta, cewar saliha wacce ta tashi cikin murna ta fita. Nasir ya kalli mahaifiyar sa da kulawa yace"umma ina yarinyar da na gaya miki cewa nakaita gidan inna? Hajiyar tace "eh na ji" "wlh pretty yau taje ta mata lahani a baya ta xuba mata ruwan zafi, inda Allah ya taimaka ma ba wani xafi ga ruwan ba" Hajiya ta gwalo ido tace "ni kuwa yaushe pretty zata yi hankali ne tukuna me ma ta mata da tayi mata wnn d'anyen aikin? Nasir yace "Kawai don tana jin haushin an hanata tuqin mota a dalilinta kuma kinsan halin pretty ta tsani talaka ba kad'an ba, cikin damuwa mamar tace "to kai nasir baza ka sallami yarinyar mutane bane ka huta, shawarar da nazo yi dake kenan umma don gsky bana son wani abu ya sake faruwa da ita duk da nayi ma pretty kashedi amma hankalina zai fi kwanciya idan ta koma ga en uwanta sae dai inna ce matsala don yanda Rayyanat ta kwanta mata a rai ba lalle bane ta yarda da hakan zata iya cewa a kaita gun en uwan Rayyanat d'in in yaso ta nemi alfarmar su bar mata ita ta riqa yi mata en wasu aikace aikace in yaso duk wata ta riqa biyanta kinga kuwa duk dai ba'a rabu ba dmn gsky nafi son Rayyanat ta komawarta gun en uwanta. umma ta nisa tace"to ya kake ganin za'ayi haka? Ya dan yi shiru snn yace "Eh to ina ganin kawai zan maida Rayyanat ba tare da sanin inna ba sae bayan na dawo na snr da ita kinga dole zata haqura. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:18PM, 1/25/2017] Ummi Ya: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 ```Na Billy giro😊``` 19/12/2016 🔮```9```🔮 To shikenan Nasir amma ina son kafin Ku tafi kazo min da yarinyar na samu abinda na bata don yarinyar ta bani tausayi wlh har dai in na tuna ko wane hali en uwanta suke ciki na rashinta oho Allah kad'ai ya sani. Wlh umma nima tunanina kenan kullum gashi taqi fad'a bare naji ko akwai lambar wayar su a kira a snr dasu halin da take ciki amma yanzu Alhmdlh tunda taji sauqi zan lalla6ata ta gaya min sae na maida ta. Nasir Yayi mgnr ne yayinda ya tashi yace "to umma ni zan tafi " Umma tace "To ka gaida innar" yace "to" snn ya fita. Nasir na fita ya nufi 6angaren su pretty ya d'auki inna dasu saliha suka wuce. Hajiyarsu pretty na fitowa daga bathroom sae ga mai gidanta ya shigo ransa a 6ace ta kalle sa da kulawa tace "lafiya Alhj me yake faruwa ne?" da taikaci ya kalle ta snn yace" ni nasara wace irin tarbiya ce kika bawa 'ya'yanki? kaf dangin nn ba wanda yakai su rashin mutunci idan suka tashi, musamman ma Fatima" nn cikin fad'an duk ya kwashe abinda inna tazo ta gaya mai har da yaron da pretty ta kad'e kwanaki don duk shi bai sani ba. A fusace ya d'ora da cewa "kiramin ita yanzun nn tazo ina son ganinta, kwata kwata daga yau ma ta daina jan mota na hanata" Umma ta dan tabe baki tace "ni dae kayi haquri Alhj, ai ba laifinta bane tsautsayi ne da kuma qaddara...." Rae bace Alhj yace "idan wnn tsautsayi ne me yakaita gidan inna har taje ta watsa ma er mutane ruwan zafi a jiki ko shima tsauyayin ne! Ku fa kiyaye ni ke da 'ya yan ki" ganin ynda ransa ya bace yasa tace "Ayi haquri Alhj bata kyauta ba dae, amma zancen tuqa mota tuni yayanta ma ya kar6e motar," Alhj yace "yayi dai dai don in kece baza Ki kar6e ba duk kinbi 'ya'ya kin lalata da baqin so sae kace kanki aka fara haifuwa. Nasir na sauke su inna gida ya wuce office bayan sun shiga gidan, saliha da Ameera suka shiga kallon Rayyanat da ke zaune ta lanqwashe qafafu tana shan fura a falon, kallo d'aya Ameera tayi mata ta kauda kai sbd ta gano ita ce yarinyar da inna taje tana faman masifa akai don a gabanta akayi komai ita da saliha. Saliha kuwa kallon Rayyanat take da d'an murmushi a fuskarta ta kalli inna tace "inna wnn itace Rayyanah?" Inna ta washe baki tace "eh ita ce er albarka babu ruwanta wlh" Saliha tace "eyyah sannu Rayyanat ya jiki?" D'an guntun murmushi tayi snn tace "Alhmdlh" a takaice. Ameera ta ta6e baki taja hannun saliha tace "ke ni tashi mu tafi gidan inna hajjo mu gaidata" (wata makociyar inna dake nn kusa bbu nisa) Inna ta washe baki tace "to in kunje ku kar6o min nono na samu na dama furar anjima" nn ta kwance ha6ar zanen ta ta basu nera d'ari tace "ku siyo na duka," Ameera ce ta kar6i kud'in tana walwale su tana dariya ganin yanda suka tamure tace "kai inna wai har yanzu baki daina dunqule kud'i a ha6ar zani ba" bata jira cewar Inna ba ta ja Saliha suka fice daga falon, sae a snn Rayyanat ta gaida inna da ladabi, inna ta amsa da fara'a tace "sae ynxu kike shan hurar, ya bayan in ga ni?" Rayyanat ta dan xuge zip din rigar jikinta inna ta duka da sauri tana kallon bayan, kmr xata yi kuka tace "Allah ya Isar maki, da bayan nn ya tashi yau da anga xube xuben ruwan xafi a jiki don duk sae na tafasa ruwa na bi ta har gidan mijinta na kona ta ni ma" Hurera dake kitchen ta fito tana dariya tace "A'a ba ayi hka ba Inna, Allah dae ya tsare" inna tace "ae ynxu ma daga gidan ubansu nake, kuma yace anjima da daddare xae xo ya gane ma idonsa" Bude kofar falon aka yi, duk suka juya don ganin wnda xae shigo, inna na ganinsa ta tsuke fuska, ya karaso falon fuskarsa a tamke, Rayyanat tayi saurin gyara rigarta, a fusace yana kallon inna ya soma magana "don me xa ki je ki hada ni da Baffana kan wata bnxa can yar kauye Hajiya," inna ta tabe baki tace "sae dae kae ne bakauye ko uwar ka amma ba yar nn ba," xaro ido yyi yana kallonta, ita ma ta yo waje da ido tace "kwarae kuwa!" Rayyanat da tun shigowarsa falon ta sunkuyar da kanta hawaye ya shiga bin kuncinta, ya huzar da iska ya cije lebe lkci daya idonsa ya kada, ya juya fuuu ya fice daga falon, inna tace "Wawa kawae." Baaba hurera ta sauke ajiyar xuciya tace "Ayi hkuri dae inna" mikewa Rayyanat tayi har lkcn hawaye na bin kuncinta, Inna na ganin hka ta rude ta shiga tambayarta lfya, Rayyanat ta kasa bata amsa, hkn yasa inna ta fashe da kuka tace "yo baki ji nace shine dan kauyen ko uwarsa ba, ni dae na shiga uku da 'ya yan kabiru" lkci daya Rayyanat ta hadiye kukan da take tace "kiyi hkuri inna, ni ba shi yasa nake kuka ba, naga ina ta hada ki da jikokin ki ne" cikin kuka ta karashe mgnr, inna ta hade rae tace "suke dae hadani da ke, kuma Allah ya fi su" Baaba hurera tayi murmushi, Rayyanat ta duka ta dauki sauran furan da take sha ta nufi kitchen. Da rana nasir ya shigo gidansa, ya nufi dakin pretty ganin bbu kowa falon ga ko ina kaca kaca, xaune ya sameta sae fushi take, yaje kusa da ita ya zauna ya shafi gefen fuskarta yace "nasha gaya miki ki daina fushi baya miki kyau," hararar sa tayi snn taja tsaki tace baka son nayi fushi shine zaka kaini qara gun daddy," Nasir ya xaro ido yace "au kin dauka nine, to inna ce taje da kanta ta gaya mai aikin da kikayi don haka ko yanzu kika sake gigin aikata wani abu akan Rayyanat zata je ta snr dashi ne," cike da bacin rae ta tashi tana masa mugun kallo tace"ni yanzu banda lokacin wnn er qauyen bare na qara kulata" ta ja dogon tsaki daga haka ta wuce fuuu! ta barshi nn zaune" girgiza kansa kawai yayi ya tashi yaje ya bud'e fridge ya tsiyaya ruwa a cup yasha. Washe gari ya gama shirin sa tsaf yaje d'akin pretty wacce yanzu ne tashinta zata shiga Bathroom dmn yin wanka. Bai qarasa inda take ba a iya gun dressing mirror ya tsaya ya ajiye mata kud'i yace "zanyi tafiya ne ban kuma san yau ko gobe zan dawo ba" ta hade rae tace "ina zaka tafi?" Ya daga kafada yace "Kina da sako ne?" daga haka yyi ficewarsa, ta6e baki tayi gami da jan tsaki tace "aikin banxa, kadda Allah yasa ka dawo ma" Nasir bai zarce ko ina ba sae gidan inna cike da niyyar ya d'auki Rayyanat ya maida ta gun en uwanta. Bbu kowa falon Inna, hkn yasa ya nemi gu ya xauna yana tunanin ynda xae fita da Rayyanat ba tare da sanin Inna ba, Baaba hurera ce ta shigo falon daga kitchen, da mamaki tace "A'a Nasiru yaushe kuma ka shigo" yyi murmushi ya gaisheta ta amsa da fara'a tana tambayarsa ya kwanan pretty, ya amsa da Alhmdllh snn yace "Baaba Rayyanat xa ki kira min amma fa kar ki bari inna tasan da ina gidan nn" tace "to bari in kirata" ba a dau lkci ba ta dawo falon Rayyanat na biye da ita a baya, hijab ne har kasa jikinta yasan inna ce ta sa aka dinko mata, ya kafa mata ido har ta karaso ta xauna kasa kanta a sunkuye ta gaishesa, ya amsa yana murmushi ya tambayeta ta tashi lfya, kai kawae ta gyada masa, bae kuma cewa komae ba har na kusan minti biyar hkn yasa ta dago kai tana kallonsa da manyan idanuwanta, murmushi ya sakar mata ta dukar da kanta da sauri, ya kira sunanta a nutse ta amsa ba tare da ta kallesa ba, yace "nasan yan uwanki na cikin tashin hnkli Rayyanat, kiyi hkuri ki gaya min ina ne garin ku" Rayyanat tayi kkrin ganin hawaye bae sakko idonta ba a karo na farko ta gaya masa sunan garin a hnkli, ya gyada kai da gamsuwa yace "to ina xa ki pretty ta kade ki da mota?" Ta girgixa masa kae da kyar tace "garinmu xan ko ma" yyi shiru snn yace "to da me ya shigo da ke kano? Shiru tayi taki cewa komae hkn yasa yace"kin shirya komawa garin naku gun yan uwanki ynxu?" Gyada masa kai tayi kawae, yyi shiru na wani lkci snn yace "to tashi ki dauko ledan kayan ki, amma kar ki Bari Inna ta ganki" tace "to" snn ta nufi dakin da Inna ta bata tana murmushi a ranta tace "don xan tafi ba yana nufin na bar shi bane, har abada baxan bar shi ba, nemo sa baxae min wahala ba tun da na ga gari." Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:18PM, 1/25/2017] Ummi Ya: 🔮```BAZANBAR SHI BA!```🔮 ```Na Billy giro😊``` 22/12/2016 🔮```10```🔮 A sanyaye Rayyanat ta dawo falon rike da ledan kayanta ta samu har nasir ya fita xuwa gun motarsa, ita kad'ai yake jira taje ta bud'e gambun motar a hnkli xata shiga ta tsaya cak jin murya inna a bayanta tana fad'in "Rayyanah me zan gani hka ina kuma zakije har da leda a hannunki?" Sake gambun motar tayi ta juya tare da sadda kanta qasa ta ki barin su had'a ido da inna, ba shiri Nasir ya fito daga cikin mota ya tsaya yana d'an kame kame sbd yanda inna ta tsare shi da ido baki bude. Kmr xata yi kuka tace " kaddai mayadda rayyanah zaka yi baka ko snr dani ba Nasiru" Ya dan sosa keya yace "Aa inna, dama wae da.." sae kuma yayi shiru. inna ta fashe da kuka tace "dama me nasiru! mayadda ita zakayi d'in knn, na rasa dalilin da yasa aka rainani hka, ynxu da bn fito ba sae dae in nemi yar nn in rasa" ta fashe da wani matsanancin kuka har da dukawa, Nasir yyi murmushi yace "kiyi hkuri Inna, kuskure ne" inna ta dago ta tsuke fuska tana kallonsa tace "rufe min baki munafuki kawae" dariya yyi yana shafa kansa yace "na yarda, amma inna baki tunanin halin da yan uwanta da iyayenta ke ciki ynxu? Ynxu misali lkci daya a nemi pretty a rasa wani hali kike tunanin xa mu shiga gaba daya" lkci daya inba ta marairaice tace "ni fa ban ce kadda a mayar da ita gun iyayenta ba, kawae rashin sanar dani da ba ayi bne ya bata min rae" Nasir yace "to ayi haquri inna," ta galla masa harara tace "yo da ban hkura ba da ban tara maka mutan anguwar nn ynxu ba," dariya yyi yana kallonta, tace "ynxu dae dani ya kamata muje gun en uwan nata su ganni nima na gansu na samu ko zasu bar min Rayyanah in rike, ni dae yarinyar ta kwanta min in sonta" ta karashe mgnr cikin kuka, tana matsar kwalla tace "ka ga idan Allah ya kawo mata miji na gari sae tayi auranta," Ba yanda nasir ya iya yace "to shiknn inna jeki d'auko mayafinki mu tafi" Inna ta washe baki ta ja hannun Rayyanah tace "zo ki rakani er albarka bazan barki a nn ba don tunda yayi niyya zan iya dawowa na samu ya tafi dake ne kawae, ko meye dalilin hkn da yyi ne oho," nn dai inna ta jata suka tafi ciki don dauko mayafinta. Har yaja mota inna bata bar mitan da take ba, hkn yasa nasir sam ya manta da zancen kaiwa umman shi Rayyanat kamar yanda ta buqata. Tafiya sukayi ba mai wani nisa sosai ba dmn da kano zuwa qauyensu awa biyu ne sae dai tun lokacin da suka kama hanya Rayyanat keta zubda qwalla a boye har suka isa. A bakin shiga garin tace da Nasir ya tsaya a nn, ya juya ya kalleta yace "garin naku ba'a shiga da mota ne?" Rayyanat ta daure tace "Ana shiga da ita amma ku sauke ni kawai nagode, zan iya qarasawa da kaina," inna ta yo waje da ido tace "yo Rayyanah ai ni en uwan naki nake son gani ko zan samu sumin alfarmar bar min ke" Shiru Rayyanat tayi hawaye suka shiga silalowa a hnkli kan kumatunta ta, inna ta saki baki tana kallonta, can tace "Rayyanah ko ba kya son komawa gu nane?" da sauri ta girgixa kanta muryarta na rawa tace "inna ni bani da kowa duk sun rasu" Inna ta rafka salati da karfi ta fashe da kuka tana cewa "wayyo ni Hajara, wayyo ni" Nasir dae yyi shiru yana kallon Rayyanat amma ya kasa yrda da abinda tace, inna ta ci kukanta ta koshi Rayyanat na taya ta kmr a lkcn aka yi mutuwar, daga karshe tana fyace majina cikin kuka tace "Allah ya rahama masu, wayyo ni rayuwa" Da kyar Nasir ya iya bude baki yace "Allah ya ji Kansu" ba don ya yrda ba gani yake kmr karya tayi masu. Cikin muryar kuka Inna yace "to nasiru muje muga mai garin nasu dmn haqqi ne akansa yasan Rayyanat zata zauna gun mu ko?" Nasir ya gyada mata kai kawae ya tada motar ya shiga tafiya a hnkli Rayyanah na nuna mai hanya har suka isa qofar mai gari. Cikin girmawa aka tarbe su mai garin yyi mamakin ganin Rayyanah ya shiga tambayarta daga ina take, nn Nasir ya dan ji dama dama gnin mai garin ya santa, bayan an gama gaggaisawa Nasir ya zayyano abinda ke tafe dasu yana kallon Rayyanah, mai gari bai musa musu ba ya amince da abinda suka buqata ya Dora da cewa suyi kkrin ganin sun riketa amana don marainiya ce sun samu lbrin rasuwan mahaifinta, Inna tace "ka ji ka da wata mgna, kasan wacece ni kuwa," mikewa tayi tana washe baki tana kallon Rayyanat tace "tashi mu je jikata, Allah xae taya ni riko" Bayan sun koma gida da kwana biyu inna ta fito cikin shirinta Rayyanat ma dake shirye cikin wani atamfa da aka dinko mata da hijab jiya tace "to Rayyanah jeki snr da hurera mu zamu fita." Rayyanat ta nufi dakin hurera, dae dae nn Man ya shigo falon yana waya murmushi dauke a lebbansa, inna ta washe haqora tace "Allahu Akbar, sannu da xuwa d'an albarka dama kmr kasan neman wanda zai kaimu anguwar nake, sae gashi Allah ya jefo min kai" Ya katse wayar da yake yana kallonta yace "kai Inna, ina xa ki cikin ranan nn" inna tace "yo ni rana da yana gasa mutum da bae gashe ni ba, kasan irin wahalar da na sha gidan mijina kuwa" ya tabe baki ya juya ya fita yace ina jiran ki a waje, tace "to to ynxu xa mu fito" tare inna suka fito da Rayyanah, yana jingine jikin motar yana jiranta don duk a tunaninsa ita da baaba hurera xa su fita, suna karaso gun motarsa ya zaro ido yana kallon innar yace "wae ke da wa xa ku fita?" Inna tace "yo Rayyanah mana" ya kuma xaro ido kmr wanda yaji abin tsoro cikin shan toka yace "nifa gasky baza ta shigar min mota ba, mgnr gskya knn, idan dai ke kad'ai ce to muje," inna ta tsuke fuska tana huci tace "yo naga ja'irin yaro, kai baka san tafiyar tata bace ma gaba daya, xuwa fa zanyi da it cikin dangi tasan kowa, kowa ya santa." Girgixa kai yyi yana masu wani irin kallo yace "to ba da motata ba, ki kira Nasir da yyi maki hanyar ta ya kai ku" inna ta fashe da kuka tana girgixa kai tace "Ni ban san meyasa bn dace da jikoki ba a rayuwa duk sun rainani uwa ba ni na haifi ubansu ba" Muhammad ya girgixa kai yana kallon innar yace "bari to in kira wani ya kai ku inna kin ga fa sauri nake" inna ta hade rae tace "A'a sae dae ka kira ubanka Kabiru ya kai mu, idan ba shi ba kam al-quran bbu motar shegen da xan shiga" Muhd ya fuxa isa ya juya yana kallon Rayyanah yace "ke shiga muje" inna tayi murmushi tace "shiga Rayyanah" kasa shiga motar Rayyanah tayi fuskarta a daure, har sae da inna tace "ki shiga nace mana" snn ta shiga inna ma ta shiga motar tana goge dan kwallar idonta tana murmushi " sae da suka hau babban titi snn Muhd ya dake yace "ina muka nufa?" Inna tace "A'a wae da gidansu Murja xaka fara kai mu, daga can sae gidansu Fatee, daga gidansu fatee sae ka kai mu gidan bari'a, daga can sae mu garxaya gidan kawata hjya Laure, in mun fito sae mu shiga gidansu Audi, to ba wani ddewa xa muyi a can ba, muna fitowa sae ka garxayo da mu gidansu Alhaji bukar, to daga gidan Alhaji bukar sae ka kai ni gidan tanko ina son gninsa, idan mun fito sae ka kai mu gidanku, daga gidanku kuma sae ka dawo da mu gida kawae don ni ban fiye son yawan gidajen mutane ba" murmushi kawae yyi yana shafa sajen fuskarsa bae ce mata komae ba. Billy Giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:18PM, 1/25/2017] Ummi Ya: 🔮```BAZANBAR SHI BA!```🔮 ```Na Billy giro😊``` 26/12/2016 🔮```11```🔮 Sae da ya kaisu duk gidajen da inna ta lissafa snn ya kaisu gidan su wato family house. 6angaren hajiyar pretty suka fara zuwa snn 6angaren su hajiyar nasir wacce ta tarbe su cikin fara'a da murna ba kamar hajiyar pretty da ta kama kallon Rayyanat a yatsine ba. Haka d'ayan 6angaren da girmamawa suka tarbi inna yayinda suke kallon Rayyanat ba yabo ba fallasa . Nan inna tabar Rayyanat amma a 6angaren su hajiyar Nasir a cewar ta musu yini. Saliha sai janta take a jiki sbd yarinyar tana da son mutane sosai ba kamar sauran yaran gidan ba hkn yasa Rayyanat ta d'an saki jikinta da saliha har ma tana jan Rayyanat da fira. inda cikin firar take ta bata labarin rayuwar su ta school , ita dai Rayyanat saurarenta kawai take ba um ba um um sae dai idan taji abin dariya tayi d'an guntun murmushinta,saliha tace "wai nikam Rayyanat kin barni ni kad'ai keta zuba kamar parrot ba kuwa zan yarda ba don kema sae kin bani naki labarin makaranta,d'an guntun murmushi Rayyanat tayi snn tace"aini banyi secondary school ba ma bare zancen boarding school,xaro ido saliha tayi tace "hm kedai ba kya son bani labari ne,a sanyaye Rayyanat tace"da gaske nake wlh" Saliha ta kalleta tace"meyasa gashi da alama zaki kai s .s 2 ko 3 inda kinci gaba?Baffana ne baya iya d'aukar nauyin karatuna" tayi maganar cike da qwallah a idonta kan tuna baffanta da tayi" Saliha tayi shiru tana kallonta sae duk taji ba dad'i tace"to ynx idan kika sami dama kina so kici gaba da karatun?girgiza kanta tayi tare da share hawayenta snn tace"ai lokaci ya qure min" lokaci bai qure miki ba Rayyanat kina da lokaci har yanzu" um um ynz ba wnn ne burina ba sae nn gaba kad'an tukun"er dariya saliha tayi tace"hm Rayyanat har wani buri kike da shi yanzu da ya wuce karatu sae dai idan karatun ne ba kya so"kallonta kawai Rayyanat tayi yayinda idanunta suka sake cikowa da qwallah ta kauda kanta gefe ba tare da tace da ita komai ba. Qofa suka ga an turo saliha ta tashi taje ta kar6i trayn abinci da ke hannun ummnta ,hjy ta bata tare da kama kunnenta ta murd'e tace"kina nn kin cika ta da baqin surutun nn naki ko kiyi tunanin d'ebo muku abinci ma bakiyi ba, dariya saliha keyi mai had'e da jin ciwo tace"wash umma Allah inada niyyar tashi na d'ebo mana abinci sae gashi kin shigo mana dashi "ta sake mata kunnen tare da fad'in"oya yi ki zuba muku abincin kuci ina so zamu d'an fita ne zuwa anjima,to umma,nn Hajiya ta fita saliha ta zuba musu abinci a plate d'aya suka fara ci sae dai basu wani ci sosai ba Rayyanat tace ya isheta sbd dama kafin su fito taci abinci. Sea bayan sllr la'asar suka fita wani qatoton mall suka je Hajiya tace da Rayyanat ta d'auki duk abinda take so, Rayyanat bata iya d'aukar komai ba sae saliha ce ta shiga d'aukar mata kayan sawa kmr su Arabian gown da turarukku designers da kuma kayan kwalliya bayan sun gama siye siyen su ne suka maida Rayyanat gida da kayanta niqi niqi wad'anda saliha ta kwasar mata, inna sae washe haqora take tana sama Hajiya albarka. 7 days later Rayyanat ce a kitchen ta gama wanke kwanika tana goge kitchen bayan ta gama ta koma d'aki. Saliha ce ta shigo gidan ta sami Mohd shida inna sae fira suke sae da ta gaishe su snn ta zauna har inna na tambayar ta ya mutanen gida tace duk suna lafiya tace"to ya na ganki yau ke kad'ai ba abokiyar yawonki Ameera? Tana gida wai yau bata jin fita tace"ayyo to ya hajiyarki tana lfy dai ko?lfiya qalau wlh ta ma ce a gaida ke,ina amsawa ai yau tama kirani a waya mun gaisa kmr kullum,eh inna Rayyanah fa? Shiga daga ciki yanzun nn ma ta shiga. Rayyanat na zaune tana duba litattanfanta na islamiya sae ga saliha ta shigo da sallamarta ,da sakin fuska Rayyanat ta tarbe ta ta nemi guri ta zauna tare da jawo littafan Rayyanat na Islamiya tace"ke yau fa Alhamis ko kin manta" Rayyanat tace"ai ba shirin zuwa makaranta nake yiba ina muraji'a ne sae gashi na sami kaina da mantuwa da wani gun a cikin littafin ishmawee babun sallati janazatee gun da ake cewa....cab ai ke ban kai babin ba wlh kad'an dai ya rage,nn taja hannunta tare da fad'in "amma muje gun yaya Man ya tuna miki kafin ya fita "cikin rashin fahimta Rayyanat tace "waye kuma haka?oops baza ki san sunan ba sbd da Muhammadu inna ke kiran shi, Man kuma complete name d'inshi ne frnds d'insa suka had'e wato Muhammad Aminullah Nasir shine har mu qannansa ke kiransa dashi sbd koda muka taso mun samu ana kiransa da sunan. Ta6e baki tayi ba tare da tace komai ba Saliha tace "muje ya tuna maki ko"um um nafi son na tuna da kaina sbd zanfi riqe abun da kyau"to amma dai zaki ajiye muraji'an nn har zuwa dare tukun sbd ina son muje ki rakani familyn mamana,a natse Rayyanat ta ware kyawawan idanuwanta tana kallon saliha snn tace"ni d'in nn? Eh man ai anguwar ba nisa da nn kuma wa ke kad'ai na biyo gidan nn wlh ,don hk ki tashi ki shirya mu tafi,nifa ban son shiga inda ban sani bane saliha ki tafi kawai abunki kinji, ,kinji Ki sae kace wacce za'a cinye dan Allah nidai tashi ki shirya mu tafi ai da sannu ake yin sabo ba wai zama zakiyi tayi kice ba kya shiga mutane ba. Turo qofar da akayi ne ya katse Rayyanat da abinda tayi niyyar fad'a,Saliha tace"yauwa inna dan Allah ina son Rayyanat xata rakani gidan Baaba. Ba musu inna ta amince da su tafi. Duk da Rayyanat bata so ba amma haka ta haqura Saliha ta tasa ta gaba tana mata kwalliya yayinda tace ta rufe idonta har sae an gama kwalliyar ko zata bud'e, byn an gama kwalliyar Rayyanat na bud'e idanuwanta ta wani ware su kan tsananin kyawon da taga tayi har ma ta fara shakkun anya ita ce kuwa tace"saliha wnn kwalliyar na tafi ina dashi nikam rage min ita don wlh ni ko kwalliya ma banayi bare na iya fita da wnn kwalliyar haka,,,um um gsky ba abinda zan rage maki , kawai don baki saba kwalliya bane kika ga kmr tayi yawa amma dai dai take, da qyar Rayyanat ta iya yarda aka bar kwalliyar saliha ta bata Arabian gown ta saka ta jawo qatoton hijabinta zata zuba saliha ta dalla mata harara da wasa tace"meye haka zan gani ki wani zuba hijabi har qasa sae kace zaki tafi islamiyya ?ban gane ba saliha to dame kike son na fita?saliha bata ce mata komai ba sae hijabin ta cire mata ta d'auko top d'in gown ta roller mata, duk da cewa Rayyanat ba wata fara bace amma shirin ya matuqar d'aukar ta sae dai faffau tace bata iya fita da shirin sae tasa hijab Saliha ta buga qasa da sama a cewar ta duba ita ma fa irin shirin ne da ita amma ina sam Rayyanat bata yarda ba, bbu ynda Saliha ta iya da ita hka ta kyaleta da hijab din suka sallami inna da ke kitchen suna wainar flower da baaba hurera, inna na ganinsu ta washe baki tace "Ma'sha Allahu" saliha tace "ku fa ajiye mana namu inna, don nasan kina iya kwashewa gaba daya ki ba ma yaya" saliha na kai wa nn ta ja hannun Rayyanat suka fice daga kitchen din, kwance suka tar da shi a falo idonsa lumshe kmr mai bacci, lkci daya ya bude ido yana kallonsu, Saliha ta dan hade rae tace "sae mun dawo yaya" Rayyanat kam kauda kai tayi ita ma fuskarta a daure, mikewa yyi xaune da sauri yace "ina xa ki?" Dauke kai tayi tace "gidan fa kaka xa mu, kuma Hajiya ta sani" kallon Rayyanat ya tsaya yi da mmki ganin ynda ta wani hade rae, can ya mike ya nufi kitchen sae ga shi ya fito inna na biye da shi a baya tana cewa "lfya me ya faru?" Sae da suka karaso cikin falon snn ya juya yana kallon innar da kyau yace "dama tambaya ce xan maki, wae wnn yarinyar me aiki ce ko ko a ina kika jajubo ta" ya fadi yana nuna Rayyanat, inna ta ja dogon tsaki ta balla masa harara tace "uwar ka ce ba me aiki ba, wnn tayi maka kama da mai aiki, hka kawae kasa ma yarinya ido a gida, uwar me ta tsare maka, to in kai maye ne sae dae ka ci kanka wllh" a fusace ya karasa gaban Rayyanah yana mata wani mugun kallo fuskarsa a daure ya dago fuskarta da kyau yana kallo, ta kuma hade rae ita ma tana kallonsa da manyan idanuwanta, a nutse ya fara mgna, "daga yau, I mean daga this vry moment kika kuma min wani irin kallo a gidan nn, ko kuma kika gan ni kika ki gaida ni sae na....." Kukan da inna ta fashe da yasa ya tura ta da karfi, ya juya yana kallon innar, kwashe wayoyinsa yyi da ke kan kujera ya juya ya fice daga falon kmr xae tashi sama, inna ta bi sa da ja'irin yaro kawai, ta karaso gun Rayyanat tana matsar kwalla tace "kiyi hkuri kin ji 'yar nn, tambada yake ji yau shi yasa yyi maki hka, amma ki kyaleni da shi, da ubansa ma xan hada sa ni ya ja masa kunne ya daina xuwa min gida don baya tsinanani da komae da ma, sae dae in dafa in basa ya ci ya bar min kwanukan a nn ya kara gaba" Rayyanah tayi murmushi kawae tace "bbu komae inna" saliha da ko kadan bata ji ddin abinda yayan nata yyi ma Rayyanah ba ta ja ta a sanyaye suka fice daga falon don xuwa inda xa su. Sae da suka fita daga gidan Saliha tace "kiyi hkuri Rayyanah hka yaya yake wani lkcn" Rayyanah tayi murmushi tace "A'a ni bn ji haushi ba wllh," saliha tace "yauwa, kuma don Allah ki dinga gaishesa in kun hadu" Murmushi kawae Rayyanat tayi bata ce komae ba, saliha tace "ke komae murmushi, ba sae ki ce min to ba" Rayyanat ta kuma yi mata murmushin tace "toh naji Saliha" saliha tayi dariya tace "yauwa ko ke fa." Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:18PM, 1/25/2017] Ummi Ya: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 ```Na Billy giro😊``` 28/12/2016 *🔮```12```🔮* Washe gari kaf gidan Rayyanat ce ta gyare shi har wajen gidan wato gun faka motoci duk sae da ta share tsaf koina ya haskaka. Snn taje kitchen don taya baaba hurera aikin abinci, baaba hurera tace "Aa Rayyanah yau kinyi aiki da yawa je kawai kiyi wanka kinsan yau juma'a qaramin lokaci ce," Rayyana tace "aa baaba bari kawai na tayaki wlh," "wlh jeki ai saura kad'an na qarasa tafi kiyi wanka kinji er albarka," cewar baaba hurera knn, murmushi kawai Rayyanat tayi ta juya ta fice daga kitchen. wanka ta je tayi ta shirya cikin riga da skirt na atamfa da inna tayi mata, sukayi mata kyau kmr ba tashin qauye ba kan yanda sukayi d'as a jikinta. qur'ani ta d'auko ta shiga karatun suratul kahfi, a dakin da inna ta bata ita kadae duk da ba kwana take ciki ba don tsoro. Tunda daga kan gate da mohd ya shigo gidan yake qare ma ko ina na gidan kallo ganin yanda gidan yayi haske yayi kyau, as in very neat ba wai don ba a share gurin ba a'a sae don ganin sharar yau ta daban ce da kullum. Faka motar sa yayi ya fito cikin motar cike da tafiyar sa ta qasaita ya isa cikin gidan yana duba agogon wrist dinsa. Inna ya samu xaune a falo ta miqe qafafu tana casbi har yana jin sautin salati na fita a bakinta, murmushi yyi hade da mata sallama, kin amsawa tayi sae ma wani kallon masifa da ta watsa mai tace "idan kasan yau ma tambad'ar ce ta kawo ka ftr min daga gida!" Muhd yayi murmushi ya karaso cikin falon tare da ajiye ledar hannunsa gefenta yana kallonta yace "ni abinci naxo ci" inna bata kula sa ba sae hannu da takai tana bud'e ledojin da ya ajiye mata 'ya'yan fruits ne da gasasshen naman rago sae gassashiyar qullin hantar rago gefe, lkci daya inna ta washe baki tace "Auu! sannu da xuwa mai gida, Allahu yyi maka albarka ya kuma nuna min aurenka" daga haka ta qwalawa Rayyanah kira. Cikin hanzari Rayyanat ta fito daga d'aki tana ganin muhd zaune ta rage saurin da take inna na washe da baki har lkcn tace "zo er albarka ki kai ma hurera 'ya'yan itacen nn ta yanyanka mana daga nn ki biyo ma maigidana da nasa abinci idan an kammala." Rayyanah tace "to" ta kar6i ledar fruit wacce sae a snn ta gaida muhd, dake bin ta da harara tun shigowarta, ba yabo ba fallasa ya amsa. Rayyanah ce ta yanka 'ya'yan fruits din da kanta ta had'o komai har da abincin mohd da inna tace, ta kawo ta ajiye ta wuce inna sae sa mata albarka take, inna ta dubi muhd washe da baki har lkcn tace "d'an albarka nn ina son muyi wata magana da kai a game da yarinyar nn Rayyanah ashe wae primary kawai tayi sae jiya nake ji a bakin saliha shine nace ka binciko min makaranta mai kyau mai tsada kabiru ya biya a sata, in yaso duk safe sae ka riqa zowa kana kai min ita, Nasir kuma yana dawo da ita idan an tashi" Wani irin murmushi yayi da jin zancen inna kamar sa6o dan har ma sae da yayi istigifari a cikin rnsa had'e da shafo sajen fuskarsa yana kallonta har lkcn murmushi dauke a lebbansa yace "to ynxu dae duk yawancin makarantu an fara jarabawan second term, kawae ki bari idan shekara ta zagayo hkn xae fi kyau" inna ta yi shiru tana kallonsa sae kuma tace "to muhammadu idan shekara ta zagayo dan Allah kar ka manta da zancen nn dan dai wlh ina son naga Rayyanah tayi karatu kmr kowa ga ta da kkri sosai in ji saliha" Yyi murmushi yace "to Allah kaimu" tace "amin" shi kuma ya jawo abinci ya fara ci. 2:30pm Rayyanat ce zaune kan carpet ta gama sallah tana addu'o'i inna ta shigo d'akin kowane hannunta yana d'auke da plate d'ayan 'ya'yan itace ne da aka yanyanka, d'ayan plate din kuma naman rago ne da kuma hanta ta ajiye tana fad'in "Rayyanah keda nace kici abinci tun da'zu ashe baki ci ba sae yanzu da na fito naga komai inda na bar shi" Rayyanat tace "yanzu dama xan tashi idan na gama sallah" "to ai kin gama sllr tashi muje kici abinci a gaban ido na don na fhmci hlnki ba kya son cin abinci" ba yanda Rayyanat ta iya ta tashi tana linke sallaya had'e da d'an guntun murmushi a fuskarta don dai ita gsky tana jin dad'in yanda inna ke kula da ita. Falo suka je inna ta kunna musu kallo Rayyanah na cin abinci suna kallon su cike da nishad'i. Washe gari ranr ta kasance ranr asabar Rayyanat tayi shirin ta tsaf na zuwa islamiya da hijabinta sky blue har qasa na islamiya ta saka safar ta klr hijabin ta d'auko niqab ta d'aura bata dai sake shi a fuskarta ta ba ta d'auko Jakarta ta islamiyya ta riqe a hannnu snn ta nufi d'akin inna ta mata sae ta dawo, inna tace "a dawo lafiya er albarka" Fuskar ta wasai ta fito d'akin ta saka takalmi ta rufe fuskarta da niqab snn ta fita, da kafa take xuwa makarantar don bbu wani nisa daga gidan can saman layi ne, yawanci duk gidajen masu da shi ne a layin don hka layin is vry cylnt, yau ma kmr kullum xaune ta gansa gaban kantamemen gate din gidan as usual, sae dae yau ba shi daya bne, shi da wani ne, bin ta yyi da kallo kmr ko da yaushe, ta wuce su da sauri tana harhardewa, ta rasa dalilin wnn kallon na mutumin nn da take gani kullum xata makaranta, ita dae fuskarta a rufe yake ko da yaushe, tsaki ta ja tana tunanin kila hanya kawae xata canxa don a rayuwarta ta tsani kallo. Har aka tashi daga makaranta bata da wani walwala, ta hada litattafan da suka yi ranan ta xuba cikin jakarta snn ta sakale shi a hannu, ta dauki Qur'an dinta ta rungume a kirji ta sallami yan kawayenta da suka dan fara sabawa a ajin ta fito ta kama hanyar gida da sauri da sauri don Karfe shidda dama suke tashi, xaune ta sami mutumin daxu har lkcn sae dae wnn karan shi kadae ne, tsallakawa tayi ta d'ayan side din ta ci gaba da tafiyarta da sauri, sae da ta dan yi nisa snn ta dan juya don ganin ko yana kallonta,Xuciyarta ya kusa shigewa cikinta ganin biyo ta ma yake, ta kara sauri gabanta na faduwa ssae, gashi bbu alamar mutum a layin, ganin duk saurinta har ya kusa cim mata yasa ta kwasa a guje ko minti biyar ba ayi ba ta isa gida har lkcn gudu take har da kukanta, mai gadi na tambayarta me ya faru bata ko sauraresa ba ta nufi kofar shiga falo da gudu, a bakin kofa suka ci karo da Muhd dake tsaye yana jujjuya makulin motarsa alamar xae tafi, suna mgna da inna, hkn yasa Rayyanat ta fasa ihu, ya koma baya da sauri lkci daya ya turata da karfi ta fadi nn kasan falon, inna ta mike da sauri ta karaso bakin kofar tana salati tana tambayar me ya faru, Rayyanat da ke mayar da numfashi ta fashe da kuka ssae, inna duk ta rude ita ma ta saka kukan ta xube nn gabanta, baaba hurera ta fito da sauri tana tambayar lfya, sae ga mai gadi shima ya taho da sauri yana tambayar me ya faru, Muhd kam don takaici komawa gefe yyi ya tsaya, cikin kuka inna ke kallon mai gadi da Baaba hurera tace "nima ban san kukan da take ba" baaba hurera ta shiga tambayar Rayyanat me ya faru, da kyar ta tsaida kukanta muryarta na rawa tace "wani mutumi ne sae yyi ta kallona idan xa ni makaranta, shine yau ya biyo ni sae na fara gudu yana ta bi na kuma" ta karashe mgnr cikin matsanancin kuka, juyawa Muhd yyi ya fice daga falon mai gadi ya bi bayansa, lkci daya inna ta tsuke fuska ta miqe tana share hawayen fuskarta tana huci tace "dan gidan uban waye shi xae biyo min ke da gudu, hurera dauko min gyale na" hurera tace "A'a inna, ba ga su Muhammadu sun fita ba" inna tace "da'alla bani mayafina in je in masa rashin mutunci" hurera ta dauko mata gyalenta ta bata, ta fixge ta fice daga falon kmr xata tashi sama, a bakin gate suka hadu da Muhd da mai gadi, Muhd yace "ina xa ki kuma inna" ba tare da ta kallesa ba tace "nemo dan iskan xan je yi mana" yace "bbu kowa a waje na duba, ita bakauyiyar wace gari ce da xata d'aga ma mutane hankali hka, kila ma harkan gabansa kawae yake xata shigo ta daga ma mutanen gida hnkli, tsiyar yan kauyen nn knn" Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:18PM, 1/25/2017] Ummi Ya: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 ```Na Billy giro😊``` 30/12/2016 🔮```13```🔮 Cikin gida suka koma tunda ba a ga wanda ake neman ba, inna dai sae masifa take tayi kmr wacce ta sami wanda ake nema a gabanta. Mohd kan takaici tun daga kan gate bai ma dawo ba jan motar sa kawai yayi yabar gidan. Inna ta rarrashi Rayyanat ta samu har ta daina kukan da take taje d'akinta ta ajiye jakarta ta cire niqab da hijab da socks ta nemi guri xata kwanta sbd har yanxu jikinta bai daina rawar tsoro ba. Inna ce ta shigo d'akin riqe da kofin fura a hannunta, ba ita tabar d'akin ba har sae da Rayyanat ta shanye furar tas. Har dare Rayyanat bata sake kmr kullum ba kallo suke amma sae tunanin gobe take idan zata je islamiya. Nasir ne ya shigo gidan da sallamar sa ,suna gama gaisawa inna ta bashi lbrn abinda ya faru da Rayyanat d'azun , ya kalli Rayyanah da kulawa yace"bai dai maki komai ba ko? Sae da ta girgiza kanta snn tace"bai min komai ba amma nasan ko gobe zan ganshi in na fita don kullum sae na ganshi idan zan tafi makaranta" ta qarashe mgnr kmr wacce zata yi kuka. Nasir ya nisa yace har da safe kike ganin sa idan zaki tafi makaranta? Aa bana ganinsa da safe sae da yamma" To shikenan da yamma zanzo kiyi tafiyar ki kar ki nuna tsoron komai don so nake na gane dalilin bibiyarki da yake,kar kisa tsoro dmn ina nn a bayanki kinji,a sanyaye ta gyad'a masa kai . Inna tace"ai kowane d'an iskan ne gobe ma kwashe ta nida shi" Nasir yace"ai ba girmanki bane inna ki barni dashi kawai"...yo shi girma ya sani ne da zai biyo er qaramar yarinya haka duk yabi ya tayar mata da hnkli gabad'aya yau ta rasa sukuni. Ai inna ina ganin irin en iskan samarin nn ne da basa da abinyi sae zaman banxa. Inna ta tsuke fuska tace"to Rayyanah kam baza tayi komai dashi ba don ya ma kama gabansa tun wuri. Nasir yayi murmushi ya sauya wata firar suka ci gaba dayi, can inna ke tambayar sa wai ina er banzar nn Fatima ta shige da na daina jin d'uriyar ta, Nasir ya shafi kansa yana murmushi snn yace"inna ai pretty ta jima bata jin dad'i sbd laulayin da take fama dashi" Dad'i inna taji sosai har da su taka rawa ta kusa samun kama kunne tace"ai bari shi kuma d'an banzan nn yazo marar son aure ,yazo yayi auren nn ko shima zanga abinda ya haifa kafin nabar duniya. Duk cikin taka rawa inna ke maganar nn Rayyanat har da er dariyar ta don rawar inna ta bata dariya sosai. Washe gari da yamma har Rayyanat taje ta dawo bata had'u da kowa ba, tare suka shigo ita da Nasir inna na ganin su ta shiga tambayar ko anga mutumin ?Nasir yace"ba muga kowa ba sae wasu masu zama gurin" wani dogon tsaki muhd dake kishingid'e yaja yace"wai inna me yasa kike biyewa bagidajiyar yarinyar nn nikam,kawai mutane na harkar gaban su ta wani ce ya biyota in miji take nema taje can qauyen su mana ta samo irinta ba tazo nn tana fakewa da wani ya biyota ba, wane kidahumi ma zata samu a nn da har zai yi lokacin ta in ba wanda uwar sa ta masa baki ba. Sosai maganar mohd tayi wa Rayyanat baqiqirin a rai duk yanda taso 6oye hawayenta sae da suka gangaro kan kumatunta tayi saurin share hawayen ta shige daga ciki ,mohd dake kallonta cikin 6acin rai sae a snn ya kauda idonsa ya maida su gun inna da ta shiga sirfa mai masifa kan yafita harkar Rayyanah har tana fad'in "sae na had'a ka da ubanka kabiru idan baka fita harkarta ba wlh. Nasir ne ya shiga bata haquri shida baaba hurera dake aiki kitchen ta jiyo fad'an ta fito" mohd kam barin gidan yayi sai haushin inna yake ji dake fifita Rayyanah akan shi har tana sako ubansa a ciki. Yau kusan kwana biyu mohd bai zo gidan inna ba inna bata damu ba sai ma harkar gabanta take. Rayyanah ce a bayan gida ta gama wankin kayanta dana inna tana shanya wacce sae ta sharce zannuwan kafin take shanyawa. inna tazo ta same ta tace"oh ni wai Rayyanah wanki kika xo kina mana keda ya kamata ace kinyi shirin islamiya !uhm inna ai na kammala yanzu zanje in shirya "to Rayyanah yi maza amma dan Allah ki daina wankin nn nasha gaya maki akwai mai min wanki har ma naki d'in duk ki daina wankewa idan sun taru ki kawo na had'a da nawa kayan na bawa abu mai wanki ya riqa wanke mana kinji. Rayyanat ta gyad'a mata kai inna ta washe baki snn tace"to yayi er albarka yi maza ki shirya ki tafi makaranta. Tafe take cike da fargaba don har yanzu bata cire ran zata sake ganin wanda ke bibiyar ta ba gashi yanxu nasir yayi tafiya bare ya rakota kmr yanda yayi mata a kwana biyun nn da suka wuce. Sai sauri take har tana hard'e qafafu jin alamar ana binta a baya dmn har sautin tafiya tana ji , kan tsananin tsoro bata iya juyawa ba sae ma duqawa tayi zata kwashi takalmanta ta banka da gudu. Sae taji an mata sallama cikin murya mai mugun taushi da sanya natsuwa ga duk wanda yaji hkn yasa ta fasa abinda tayi niyya sae dai cike da 6acin rai ta miqe dmn ganin wanda ke neman takurata a rayuwa. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:18PM, 1/25/2017] Ummi Ya: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 ```Na Billy giro😊``` 30/12/2016 🔮```14```🔮 Murmushi ya sakar mata duk da ba ganin fuskar tata yake ba kansancewar niqab d'inda ke sanye da ita. Kafin ya ce komai ta buga mai uban tsaki tace"wai malam lfy kake faman bibiyar rayuwata!wani murmushi ya sake sakar mata yakai hannu cike da natsuwa ya shafo sumar kanshi snn yace"sbd ina sonki"harara ta dallah mai had'e da tsaki "ta tafi ta barshi nn tsaye, Bai bita ba sae tsayuwar sa ya gyara tare da hard'e hannuwan sa a qirji yana kallonta har ta 6ace ma ganin sa. Juyowar da zaiyi ne sukayi ido hud'u da Man dake masa wani mugun kallo na tsana yace"kai amma ka bani kunya wlh kai yanxu baka ga abin bibiya ba sae wnn abar "uhm man kenan wnn ce abar yrnyr da ta koina ta amsa kiran mace har mace ga natsuwa da kamala .....mtsw! Man yaja tsaki yace"ga dukkan alama ka fara shaye shaye shiyasa kake ganin abu baibai,nn ya tafi ya barshi kmr wanda zai tashi sama. Gidan inna ya nufa ya sami inna da baaba hurera zaune a tsakiyar gidan suna fira. Ya gaida su sae baaba hurera kad'ai ce ta amsa gaisuwar , inna dake harararsa ganin zai shigar mata d'aki tace"me kuma zakayi min a cikin d'aki bayan duk gamu nn a waje"baaba hurera tace"ke ko dai inna mai gida ne fa ai kya tashi ku shiga ciki kiji dame yazo, ai nasan ba abinda yazo dashi face tambad'a da iya shege,ni kwana biyun nn ma da baka zo ba sae naji sat kmr an cire min qaya. Kujerar zaman mata naga man ya jawo wacce su inna ke zaune kan irinta yasa farin handkerchief d'insa ya share snn ya zauna yana fuskantar inna d'auke da murmushi a fuskar sa yace"ashe inna in na mutu kin huta dani kenan... zaro ido tayi tace"me kuma ya kawo zancen mutuwa ana zaune qalau, to inna ke kika ce kinji dad'i da banzo kwana biyun nn ba, yo dan nace haka Muhammadu ai bazan yi ftr ka mutu ba nida nake son ganin 'ya'yanka kafin na bar duniya tukuna ma wai kai don ubanka yaushe zakayi auren ne kullum kana mana yawo da hnkli baka ko son ana zancen, ni ka gaya min idan kana fama da rashin lafiya ne inji dan insan ta inda zan fara nemar ma magani, sajen fuskar sa ya shafo yana kallon inna wanda har lokacin da murmushi d'auke a fuskar sa yace"inna me kuka dafa yau? Ban sani ba ina ma magana kana wani zancen, oh ni Hajara wai ko dai muhamnadu gamo kayi da aljana da duk ana ma zancen aure sae ka canza da wata maganar,ta qarashe mgnr cikin kuka irin na tsafi d'in nn, mohd ya kalle ta da kulawa yace"nifa inna kinsan na tsani na ganki kina kuka indai aure ne nayi kusa nn bada jimawa ba inshaAllah" Kai zo kuka farin ciki gun inna har da su rawa tana yiwa man kari kan irin farin cikin da yasa ta yau ta jashi zuwa d'aki sae zuba masa albarka take yayinda baaba hurera tabi su da kallo tana dariya dn har lokacin inna rawa take man kuwa sae murmushi yake don shi yana son ko yaushe yaga inna cikin farin ciki . Inna da kanta taje ta kawo mai abinci wacce yinin rnr duk cikin farin ciki tayi shi. 6:5pm Rayyanat ce ta shigo gidan ta dawo daga makaranta ta sami man kwance a falo kan 3 seater kmr mai bacci don idanuwan sa a rufe suke, tsaye tayi tare da yaye niqab d'in fuskar ta tana masa kallo mai cike da tsana, karaf idanuwansu suka had'u tayi saurin kauda idonta tare da gaishe shi ba tare da ta damu da ya amsa ko kar ya amsa ba tayi ficewar ta zuwa d'akinta. Da sauri man ya tashi ya bita ya finciko hannunta da qarfin tsiya har sae da jikinsu ya had'u sae kuma yayi saurin ture ta daga jikin nashi ya nuna ta da yatsa yana fad'in"ba nayi warning d'inki kan wnn d'an iskan kallon da kike min ba ,wlh ina mai gaya miki duk na qara kama ki kina min irin wnn kallon na lafira sae yafi ki jin d'adi!dan ubanki inni sa'anki ne ko kuma abokin wasarki! Zama d'aya qwalla ta ciko a idon Rayyanah kan jin zafin zagin da ya mata,ta d'ago tana kallonsa haka shima kallonta yake har hawaye suka fara sakkowa a hnkli kan kumatunta . Ya watsa mata mugun kallo snn ya bar d'akin Rayyanah kuwa share hawayenta tayi snn ta ajiye jakar hannunta ta cire hijab da socks ta kai su a muhallinsu. Tayi zamanta a d'aki har sae da ta tabbatar mohd ya bar gidan snn ta fito taje d'akin inna wacce tana ganinta ta washe baki tana tarbon ta da murna kyace ta kwana bata ganta bane. Bayan sati d'aya da faruwar haka Mohd ne zaune a office d'insa yana waya kan cewa "a bashi ixini ya shigo"ya ajiye wyr ba jimawa aka turo qofa ya kafe wanda ya shigo da ido har ya zauna. Hannu suka bawa juna suka gaisa snn wanda ya shigo ke cewa"Man magana naxo muyi mai muhimmanci kuma dan Allah kar kayi poking d'ina"man dake jingine ya lumshe ido tare da sauke ajiyar zuciya snn yace"ina jinka" Kallon sa yayi da kyau yace"about wnn yarinyar ne da nake bibiya idan zata tafi islamiya ashe ma ka santa"da sauri man ya bud'e idonsa dake rufe yace"aka ce maka na santa who say so? Nop ba wanda yace kawai ni naga hkn sbd a kullum gidan inna nake ganin tana shiga haka kuma gidan take fitowa"to ban santa ba nima ganinta kawai nake a gidan" A sanyaye mutumin yace"to naji ganin ta kawai kake da haka nake so ka taimaka min kamin jagora muje ko yrnyr nn zata fara kulani dmn wlh nayi nayi ta kulani taqi gashi ni kuma dgske nake sonta wlh" Man da tunda ya fara zancen sa yake masa kallon ka ta6u yaja dogon tsaki tare da girgiza kansa yace"tabbas munir ynx na tabbatar ka fara shaye shaye amma ka 6ata kanka wlh ka kuma cuci iyayenka da tarbiyar da suka maka" Cikin damuwa munir yace"wai Man meye hk duk a cikin frnds kafi kowa sanin halina fa....banda yanzu da ka sauya halayen ka don haka ni ka ma ftr min daga office,pls man.... Munir!nace ka fita ko! Cikin 6acin rai munir ya tashi ya fita ya bar mohd dake juyi a hnkli kan kujerarsa yaja guntun tsaki yace"na rasa wace irin qwaya ce yake sha dake sauya mai tunani gabad'aya da har ya fad'a jin son wnn abar har ma wai yake cewa na masa jagora sae kace ni d'an makauniya ne ko makaho" Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:18PM, 1/25/2017] Ummi Ya: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 ```Na Billy giro😊``` 1/1/2017 🔮```15```🔮 Munir yaro ne kyakkyawa mai matuqar mutunci da kamala haka kuma yaro ne mai girmama manyansa ya kasance mai tausayin talakawa sosai sbd haka ya taso ya sami iyayen shi da son taimakon talakawa duk da irin kud'in sa kuwa basa da wulaqanci ko kad'an asali ma gidan su munir gida ne da ko yaushe zaka sami jama'a wad'anda ake bawa taimako. Su biyar ne a gun iyayen su ,shine na farko snn hameed ,Hasheem,Hafsat snn er autar su safiyya. Munir ya jima yana son yayi aure amma bai sami wacce ta kwanta mai a rai ba sae akan Rayyanat wacce ko da kuskure bai ta6a ganin fuskarta ba amma rnr farko da ya fara ganin ta yaji ta kwanta mai a rai ya kuma ji a ransa irin matar da yake son aura ce. Ranar alhamis ba islamiya hakan yasa Rayyanat tayi zaune tana ta mitar littafanta, ita kad'ai ce a falon tana karantawa da larabci tana fassarawa tamkar tana a gaban malami yanda ta taqarqare. Ba komai yasa taxo falo tana yin karatun ba sae don inna ta fita anguwa baaba hurera kuma tana kitchen,gashi inna tace xa'a kawo saqo shiyasa taxo falo ta zauna kar wanda inna tace zai zo ya kawo saqo yazo basu ji ba. Rayyanah yarinya ce mai tattara hnklinta gabad'aya akan abinda ta sa ma gaba hkn yasa bata san da shigowar Mohd ba duk da kuwa sallamar da yayi sae ganin mutum kawai tayi tsaye a kanta, a tsorace ta saki ihu tare da jefar da littafanda ke hannunta zata kwasa da gudu kenan man ya dakatar da ita cikin daka mata tsawa, sae kawai ta fashe masa da kuka tana kallon shi ,wacce sae a snn ta gane waye,ai kuwa kai tsaye ta had'e girar sama da ta qasa tare da share hawayen fuskarta, Mohd kuwa tsaki yaja yayi tsaye yana kallonta yayinda hannyen sa ke cikin aljihun wandonsa,ciki ciki ta gaida shi ta duqa ta kwashi littafan ta ta wuce ta kaisu d'akinta ta ajiye snn ta nufi kitchen dai dai baaba hurera ta shigo ta qofar baya duk a rud'e, tace"Rayyanah ba kece naji ihun ki ba ina bayi? Kmr wata qaramar yarinya ta 6ata fuskarta tace"nice Baaba wnn d'in nn ne ya shigo ban sani ba sae ganin sa nayi shine na tsorata" Baaba hurera tace"waye kuma wnn d'in nn ?Rayyanah tace"wnn d'in nn dake zuwa gun inna kullum. Baaba hurare kam bata gane ba sae falo ta tafi dan ganewa idonta , tana ganin mohd ta washe baki snn tace"ayyo wai muhammadu kaine Rayyanah ke cewa wnn d'in nn sae duk ban gane ba shine nace bara na fito naga waye. Murmushi ya sakar mata tare da gaida ta snn yace"inna fa na shiga d'akin nata ban same ta ba" Baaba hurera da har lokacin murmushi take tace"ai ta d'an fita ne ita da Nasiru amma tace bazata jima ba zata duba Fatima (pretty) ne dake jin jiki,to Baaba ace da wnn yrnyr ta kawo min abinci na,Baaba hurera tace "to"snn ta koma kitchen ta snr da Rayyanat. Tun daga qofar kitchen mohd ya tsare Rayyanat da mugun kallo har ta qaraso ta ajiye masa abinci zata juya yace"ke xo nn" Juyowa tayi tare da watsa masa manyan idanuwanta a cikin nashi, guntun tsaki yayi ya kauda nashi idanun sae kuma ya sake kallonta snn yace"wae ke wace ce da kika raina ni haka meye matsalar ki dani?kauda idonta kawai tayi ba tare da tace dashi komai ba, ya saki tsaki yace"tafi ki bani guri amma wlh duk rnr da na qara jin kince min wnn d'in nn sae bakin ki ya gaya miki" Ta juyo had'e da ta6e baki ta fara tako kenan taji yo sallama ta amsa sallamar ta tafi ta kar6o saqo , kitchen ta tafi da saqon dan inna ta gaya mata abinda za'a kawo wato nmn kaji,tas Rayyanat ta wanke nmn ta zuba a freezer. Washe gari rnr juma'a Rayyanat taci er kwalliyarta ta juma'a tana zaune abinta a d'aki ta gama karatun srtl kahfi ta jawo litattafanta na islamiya tana mita. Tana cikin haka taji inna na qwala mata kira ta fito da sauri taje falo ta sami inna dasu saliha da Ameera nn ta saki fuska suka gaisa da saliha akasin Ameera da ta qi ko kallon gefen Rayyanat. Inna ta kalli Rayyanat washe da baki tace"dama yanzu nake shirin kiranki kixo kici abinci sae ga su saliha sun shigo kinga sae kije ki d'ebo maku abincin kuci tare" Rayyanat taje ta d'ebo masu abinci a qaton plate , fried rice ce da akayita ta da qoda tayi kyau sosai har ta gaji d'auke da paper chicken da aka d'ora a gefe. A nn falon sukayi zaune zasu ci , saliha ta kalli Ameera wacce ta maida hnkli kan TV bata da niyyar tasowa suci abinci ,tace"Ameera taso muci abinci ke muke jira fa"da d'an mamaki Ameera ta kalli saliha snn ta nuna kanta da yatsa tace"ni d'in nn'sae kuma ta wani yamutse fuska tana kallon Rayyanat kmr wata abar qyama tace"kuci kawai ni a qoshe nake sae dai zuwa anjima ko zanci"kafin saliha tace komai inna tace"kinga bana son iya shege tashi kuje kici cikin taro ai yafi" Wlh inna a qoshe nake sae dai zuwa anjima,ke kika sani cewar saliha wacce tuni ta fhmci dalilin da yasa Ameera taqi tasowa suci abincin. Suna cikin cin abinci saliha ke cewa "yauwa Ameera idan mun qarasa cin abinci ina son muje ki rakani gidan su yaya munir gun safiyya na kar6o house wears d'ina sbd dai dai su nake son amin sabbin da za'a d'inka min" Ameera tace"to gama d'in muje ko banza ina son naje naga safiyya" Wlh kam safiyya nada qoqarin ziyartarmu"cewar saliha wacce ta kalli Rayyanat tace"tare fa zamuje dan ki hanzarta cin abinci naga sae ci kike kmr ba kya so"Rayyanat tayi murmushi tace"to so kike ina cin abinci sauri sauri naje har ya sarqe ni ai komai sannu a hnkli yafi" Murmushi saliha tayi tana mai kallon Rayyanat tace"hakane amma kin fiye shiririta gun cin abincin naki in nice ma sae ya girshe ni kafin na qoshi, shiyasa nake sauri abuna sae na kammala cin abincin ina mai marmarin sa don nafi son haka,kema idan kika gwada yin haka zaki fi jin dad'i. A sanyaye Rayyanat ta kalli saliha tace"har abada bana son sauya tsarin cin abinci na sbd haka na taso na sami Abbana yana ciyadda ni. Tana kawowa nn hawaye suka sakko kan kumatun ta tayi saurin tashi ta bar gurin yayinda saliha ta bita da ido cike da tausayi. Ameera ta ta6e baki tace"kukan name kuma ana zaune qalau? Ajiyar zuciya saliha ta sauke tace"bari kawai Ameera wlh Rayyanat abin tausayi ce dmn ta bani labarin rayuwarta ciki har da mutuwar mahaifinta da shi kad'ai ne gatan ta a duniya kinga dole tayi kuka a duk lokacin da ta tuna shi,Ameera ta wani ta6e baki tace" to Allah ji qan mamata" Amin cewar saliha wacce ta tashi taje ta lallaso Rayyanat ta shiryo suka fito . Ameera kam ganin da Rayyanat za a tafi tace ta fasa bata zuwa su dai gaida safiyya, ko kad'an saliha bata damu ba duk da ta fhmci dalilinta. Inna suka je sukayiwa sallama suka fita ta bisu da Allah dawo daku lafiya. Gidan ba nisa sosai dan qasa ma suka bi ,suna shiga gidan Rayyanat ta tsaya ta kasa shiga ba don komai ba sae don hango munir da tayi zai shiga mota, sosai gabanta ya fad'i don ta rasa wane irin mutum ne shi da duk inda taje sae ta had'u dashi. Saliha ce ta riqo hannunta tana fad'in"zo muje mana" Haka Rayyanat ta dake tabi saliha sbd tasan idan ba gamo tayi ba ba zai gane taba tunda kullum cikin niqab yake ganinta. Da sauri ta sadda kanta qasa ganin irin kallon da yake mata har ma ya fasa shiga mota ya nufo su yazo ya tsaya gab da ita,gam ta qara riqe saliha dmn ta gama yarda gamo tayi, saliha kuwa sae washe baki tayi tana kallon munir tace"yaya munir ina wuni? Fuskar sa wasai ya amsa mata har yana tmbyr ya su umma tace"duk suna lafiya. nn taja Rayyanah zasu wuce, yayi saurin dakatar da ita kan cewa "ki shiga kawai qawar ki zata same ki daga baya" da qyar saliha ta iya qwace hannunta daga na Rayyanat ta tafi ta barsu d'auke da murmushi a fuskarta. Da hanzari Rayyanat ke qoqarin bin saliha munir yayi saurin shan gabanta yace"yau kam ba inda zaki sae kin saurareni" Kuka kawai ta fashe masa dashi dan gabad'aya ta gama tsorata dashi. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:18PM, 1/25/2017] Ummi Ya: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 ```Na Billy giro😊``` 2/1/2017 🔮```16```🔮 Cikin muryar sa mai saka natsuwa ya shiga bata haquri har ta tsagaita kukanta da takeyi marar sauti. Cikin kulawa ya kalleta da kyau snn yace"kin tsorata dani ko shiyasa kike kuka,ko kad'an baki da laifi a bisa tsoratar da kikayi sbd ban ta6a ganin fuskar ki ba amma yau ina ganin ki na gane kece , kin san sbd me na gane ki? D'agowa tayi tana kallon shi , Shi kuma kmr wanda ke tsaye da er shekara shida yace"to yi min magana man sae na gaya miki" A sanyaye tace"sae ka fad'a" Murmushi yayi tare da nuna gefen zuciyar sa yace"ta nn na gane kece sbd duk lokacinda na gnki zaki tafi islamiyya bugun xuciyata ya kan canxa har sae kin 6acewa gani na,shiyasa nake tunanin idan na rasa ki ya zanyi dmn nasan zuciyata zata iya lalacewa ta bar jikina,da haka nake roqon ki kan dan Allah ki amince dani kinji. Kallon sa tayi shaye da toka tace"kaga malam ni zan shiga ciki" Sosai ya langwa6ar da kansa cike da son kora mata wani bayani tayi saurin girgiza kanta alamar bazata saurare shi ba ta kuma kama hnya ta bar gidan sae kiranta yake yana rarrashi kan ta dawo ya shigar da ita cikin gida amma fafau taqi tsayawa. Tana isa gida dai dai ta kai tsakiyar falo sae kawai taji ta fashe da kukan da ta rasa dalilinsa ai kuwa da gudu ta shige d'akinta don bata son wani yaga tana kuka,sbd sam hnklinta bai bata ganin kowa a falon ba alhali kuwa Mohd da Ameera suna nn zaune. Ameera ta kalli mohd da ya tsure qofar Rayyanat da kallo kmr mai wani nazari can ya maida duban sa ga Amira yace"ita wnn daga ina ta fito? ta6e baki tayi snn tace"gidan su yaya munir ta raka saliha ,saurin kallonta yayi jin gidan da ta ambata ita kuma ta qarasa da cewa"wata qil qauyanci ta nuna musu shiyasa suka koro ta" Komai bai ce mata ba sae tashi yayi ya fita. Rayyanat na cikin kukanta taji an turo qofa tayi saurin tashi ta share hawayenta ,saliha wacce ta shigo taxo gab da ita ta zauna ta riqo hannyenta cikin murya mai kama da ta rarrashi tace"haba Rayyanat meyasa kike ma yaya munir haka yace tsawon lokaci yake bibiyarki amma kinqi ki saurare shi,don Allah Rayyanat ki taimaki yaya munir wlh na fhmci mugun sonki yake ,Hawaye ne suka gangaro kan kumatun Rayyanat tace"saliha ki bawa yayanki haquri dmn tunda yaya anwar ya mutu na ajiye soyayya ba kuma zan qara ba ko banza ma bazan iya soyayya da mutumin birni ba ,meyasa zaki ce haka Rayyanat naga ko yaya anwar a labarin ki da kika bani shi d'an birni ne,eh amma shi asalinsa d'an qauyen mu ne nace maki ba tashin birni bane ,amma Rayyanat d'an birni da na qauya ai duk abu d'aya ne dmn duk Allah ya yisu'"um um ba d'aya bane saliha,akan me zaki ce haka? Sbd ba d'aya bane,ajiyar zuciya saliha ta sauke tana mai kallon Rayyanat tace"indai hali kike tunani to wlh yaya munir yana da halin kirki....a zahiri ba dmn baki san meye bad'inin sa ba" amma kinji ance labarin zuciya a tambayi fuska "banda hali saliha ba kuma xaki gane dalilin da yasa na tsani d'an birni ba sae nn gaba,da mamaki saliha tace"tsana kuma,to wani abu d'an birni ya miki ne dmn naga a cikin labarinki anwar kad'ai ne d'an birni kuma kince lfy kuka rabu dashi asali ma in rashin mutnci ne ai d'an qauyen naku ya muku wato bala da yasa kuka koma daji da zama,ko kuma kin 6oye min wani abu a labarinki ne?idanuwan Rayyanat tap da qwallah take kallon saliha tace"Saliha ki daina min tambayoyi haka don Allah" Saliha ta nisa tace "shike nn amma ga dukkan alamu ba duka kika gaya min labarinki ba"shiru Rayyanat tayi dmn tasan tabbas bata snr da saliha dalilin mutuwar Baffanta ba kawai dai tace mata ya rasu. Tace"hm saliha ki yarda dani mana ni ban rage miki komai ba a labarina ba,kawai dai bana ra'ayin soyayya har da d'an qauyen ma dmn tunda yaya anwar ya mutu naji bazan iya soyayya da duk wani d'a namiji ba wnn alqawari ne nayiwa kaina dmn inaji idan na kula wani tmkr nayiwa yaya anwar butulce ne. Hm Rayyanat kenan kina nufin haka zaki tabbata ba aure, d'an guntun murmushi Rayyanat tayi snn tace"To ce maki akayi rayuwar tawa tsawo ne da ita nida ma nake roqon Allah yasa rayuwata zata kai ga na cika burina" hm har akwai wani buri a gun 'ya mace da ya wuce aure? Kallonta kawai Rayyanat tayi ta kauda kanta,snn tace"inada wnn burin amma a da wato kafin yaya anwar ya mutu. saliha tace"nidai Rayyanat al'amuranki na bani mamaki rayuwar ki idan mutum ya kalla kmr so simple n easy amma ashe in kika dake kan abu kin dake kenan. Ba hk bane saliha yaya anwar yana da matuqar muhimmancin da bazan iya kula kowa ba. Cikin nuna 6acin rai saliha ta tashi tace"tunda haka kikace shikenan shi kuma yaya munir Allah ya bashi wacce ta fiki da komai ma" Nn ta fito falo ta sami mohd zaune yana cin abinci ya tsare ta da ido kmr wani mai tuhumar ta,ta sadda kanta qasa tare da gaida shi snn tace da Ameera tashi muje gida ,nn ta tashi sukayi wa inna sallama zasu fita mohd ya kira saliha tare da zaro kud'i a aljihunsa, saliha taxo cike da ladabi, Ameera kuwa ta biyota cikin rawar kai , mohd ya dalla mata harara yace"bana son shisshiga fa ke na kira ko saliha" kmr zata yi kuka tace"saliha" Girgiza kansa kawai yayi had'e da d'an guntun tsaki don ko kad'an baya son hali irin na Ameera nn ya miqawa saliha two thousand a cewar suyi kud'in a daidaita tayi masa godiya suka wuce. Bayan ya kammala cin abinci yaje d'akin inna zai mata sallama inna dake zaune tana lazimi tace"yauwa d'an albarka yanzu nake qoqarin tashi na same ka,sbd ina son zamu yi wata magana mai muhimmanci da kai,a natse man ya zauna kan gefen gadon inna yace"ina jinki inna". Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:18PM, 1/25/2017] Ummi Ya: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 ```Na Billy giro😊``` 3/1/2017 🔮```17```🔮 Muhammadu tafiya nake son zanyi a cikin satin nn zuwa qauyen mu dmn na jima rabona da zuwa shine nake son zan kai Rayyanah a can gidan ku har idan na dawo. A natse mohd ya d'ago yana kallonta snn yace"shike nn inna amma kinyi magana dasu Abba kuwa.....Yo sae da izinin su zanyi tafiyar ne ko kuwa Rayyanah d'in ce baka son ta zauna gidan naku! Ba haka bane inna sanin dai nayi tafiyar ki idan kika yita sae wanda ya ganki,inna ta washe baki tace"ayyo ai muhammadu kasan en uwa dad'i ne dasu shiyasa nake d'an jimawa idan naje. To inna wace rnr zaki tafi? Eh to rnr laraba nake son na tafi in Allah yaso,to Allah ya kaimu lokacin inna, Amin Amin d'an Albarka. Tare suka fito shida inna ta nufi d'akin Rayyanat shi kuma ya fita daga gidan. Zancen tafiyarta ne taje ta snr da Rayyanat ta fita ta bar Rayyanat cikin rashin jin dad'i da tunani sae take jin kmr kar inna tayi tafiyar nn ba don komai ba sae don sabon da tayi da inna. Bayan kwana uku da faruwar haka cikin ikon Allah ynx munir ya fara shawo kan Rayyanat dan yanzu har tana d'an tsayi ta saurare shi. Ko yauma tafe suke ta dawo daga islamiyya sae janta yake da fira ita dai iyakarta murmushi da kuma wasa da en yatsunta. Har qofar gida ya rakota tana shiga gidan sae ga Muhummad ya fito zai tafi masallaci dan har an fara kirayen kirayen sllr magrib. Cikin sakin fuska munir ya miqa masa hannu suka gaisa inda shaye da toka man ya zare hannun sa daga na munir ya wuce, munir ya bisa da murmushi dmn inda sabo ya saba da halin abokin nasa. munir yaje ya nemi buta yayi arwala ya shiga masallaci sbd dama masallacin kusa da gidan yake . Rayyanat kuwa tana shiga gida ta cire hijab, niqab da socks, ta jawo er akwatin ta da inna ta saya mata,ta ciro kayanta a wardrobe tana tsarawa da yake fashin sallah take shiyasa bata yi zancen sallah ba. Komai da tasan zata buqata sae da ta zuba a ciki snn tayi zaune tana tunanin yanda zata yi rayuwa a gidan su man , sae roqon Allah take a ranta kan Allah yasa 6angaren su saliha zata zauna in hkne kam da sauqi. Guraren qarfe takwas da rabi zaune suke a falo ita da inna suna cin abinci suna kallo inna tace"Rayyanah ina ce kin harhad'a kayanki dan kinsan na gaya miki sammako zanyi shiyasa ma na sallami baaba hurera tun yau, eh inna na harhad'a komai tun d'azun, tayi mgnr ne a sanyaye,inna kuwa ta washe haqora tace"to Allah miki albarka 'yannan idan kinje ki sakin jikin ki sosai don tamkar gidan ku ne kinji, Rayyanat ta gyad'a kanta wanda yayi dai dai da shigowar nasir d'auke da sallama a bakin shi, inna ce ta amsa masa sallama, Rayyanat kuwa ta gaida shi cikin ladabi snn ta d'auki kwanon tuwonta ta shiga daga ciki. Nasir kuwa bayan ya amsa gaisuwar Rayyanat ya gaida inna wacce ta amsa gaisuwar washe da baki snn tace"ka dai ji zancen tafiyar tamu yanda na snr da kai a waya ko, eh inna inshaAllah tunda sassafe zaki ganni,tace "amma fa ina son sae mun sauke Rayyanah a gidan naku, eh inna ai duk kin snr dani hk a waya. To ya jikin Fatima da sauqi dai ko, wlh Alhmdlh inna taji sauqi sosai don harma tana cin abinci yanxu, to madallah Allah ya nuna mana ta sauke abinda ke cikin cikinta lafiya ,Amin amin inna. Daga haka suka ta6a er fira , guraren tara da rabi snn ya wuce. Washe gari tun da safe nasir yazo ya kwashi inna da Rayyanah suka tafi gidan nasu, inna taje kowane 6angare ta musu bankwana wacce duk 6angaren da taje tana riqe da hannun Rayyanah har saida tazo gun mota zata shiga snn ta saki hannun Rayyant tana mata sae ta dawo. Su inna na wucewa Rayyanh ta ajiye kuka amma marar sauti,mohd dake tsaye sae kallonta yake don ya fahimci ba qaramar shagwa6a Rayyant zata yi ba. Shida kanshi ya ja mata akwatin ta suka tafi 6angaren su,yana tafe Rayyant na bayanshi har suka tafi d'akin Ameera,sae da ya kalli Rayyanat ganin har lokacin kuka take snn ya kai hannu a hnkli ya fara qwanqwasa qofar. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:18PM, 1/25/2017] Ummi Ya: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 ```Na Billy giro😊``` 4/1/2017 🔮```18```🔮 Ya jima yana knocking snn aka bud'e qofar,wani mugun kallo ya watsa ma Ameera wacce ta fito cike da jin bacci sae miqa take ,tayi saurin daina miqar ganin kallonda yayanta ke mata, kmr da tsoro tace"yi haquri yaya ina bacci koda kake ta qwanqwasa min,bai ce da ita komai ba sae akwatin Rayyanat ya miqa mata tare da fad'in"ki ware mata gurin da zata saka kayanta a nn zata zauna har sae inna ta dawo. Ba musu ta kar6i akwatin ta shigar da ita mohd kuwa ba tare da ya kalli Rynt ba yace"shiga daga ciki idan kika buqaci wani abu ki snr da ita Ameeran, daga haka ya wuce ita kuma tasa qafa zata shiga dai dai Ameera zata fito sae qunquni take ta bangaji rynt da qarfi har sae da ta nemi fad'uwa bata damu ba don dama da niya tayi snn tayi ficewarta sae d'akin hjyr su. Ta shiga cikin kuka mai d'auke da shagwa6a tace"umma wlh ni bazan iya rayuwa da wnn yrnyr a d'aki d'aya ba, xaro ido Umma tayi tace"au wai a 6angaren nn zata zauna?eh yaya ne ya kawota wae har sae inna ta dawo daga qauye,ta qarashe mgnr cikin muryar kuka sosai snn ta d'ora da cewa"gsky umma ni d'akin masu aiki zan maida ta dn tafi cancanta a can"Umma ta nisa tace"kinsan hln yayanki ko dukan ki zai iyayi akan haka dn yafi son duk inda ya ajiye abu to yazo ya same sa a nn"uhm uhm umma dan Allah nidai ki masa magana ya sauya mata wani d'akin ai akwai d'akunan baqi ma,to shike nn zan masa magana,nn Ameera ta fita tana mai share qwallah. Tana zuwa d'aki ta sami Rynt tsaye riqe da akwatin ta ,ta kalle ta a wulaqance snn tace" fita waje ki jira yaya zai zo ya baki wani d'akin, ba musu Rynt taja akwatin ta ta fita don sae ftr take ma a sauya mata 6angaren gabad'aya. Ta jima tsaye a bakin qofar Ameera kuwa tuni ta shige blanket ta koma bacci. Ganin ta gaji da tsayuwa yasa ta rage tsawonta bata jima da haka ba sae ga man ya shigo 6angaren cikin shirin sa na fita aiki yayi tsaye da mamaki yana kallonta snn yace"ke ba cewa nayi ki shiga ciki ba shine sbd qauyanci kika yiwa mutane durqushe a bakin qofa!shaye da toka ta d'ago tana kallon sa snn tace"to ai bayan na shiga wnn qanwar taka tace wai na fito zaka canza min d'aki" Komai bai ce mata ba sae kutsa kai yayi ya shiga d'akin sae ihun Ameera taji ta fito aguje tana kuka awa wacce aka fasawa kai wanda hkn yasa iyayensu suka fito a rud'e , ta tafi da gudu jikin umma tana kuka Abbansu yace" lfy me yake faruwa ?Abba yaya ne ya mareni ban masa komai ba, Abba ya kalli mohd da ya fito yace"me Ameera ta maka ne wae? Abba kunfa san hln Ameera ta iya wa mutum qarya da fad'ar abinda ba'ayi ba,shine wae yau har abin ya fara kawowa kaina!nn ya matsa gab da Ameera kmr wanda zai bugota yace"yaushe nayi dake zan canza mata d'aki!dake nake magana ki bani amsa koni sa'anki ne! a razane tace"yi haquri yaya wlh qarya na mata baka yi dani haka ba.....er iska yrny wlh duk rnr da kika qara fad'ar abinda bance ba sae nayi maganinki fiye da na yau, daga haka ya wuce kmr wanda zai tashi sama. Abba ya sauke ajiyar zuciya yace da Rynt shiga ki ajiye kayanki. Umma kuwa taja Ameera suka tafi d'aki sae fad'a take mata tana fad'in keda nace zan masa magana me kuma ya kaiki yin haka gashi ynx kin 6arar da komai don yanzu dole ki zauna da ita d'aki d'aya ba kuwa zan nema maki alfarmar sa ba, Ameera dai sae kuka take bata ce komai ba don tasan ta riga da ta jama kanta. Rayyanat na shiga d'akin ta nemi guri ta ajiye akwatin ta snn ta kalli agogon bangon da ke d'akin qarfe tara da rabi time d'in islamiyya ya tafi don ta makara sae dai zuwa yamma sae duk bata ji dad'i ba hkn yasa ta ciro littafanta tana mita. Kwana Rynt hud'u a gidan kullum sae Ameera ta nemi tayi fad'a da ita amma tana basarwa duk da tana jin zafin abubuwan da take mata kuwa. Haka kwata kwata hjy bata sakar mata fuska ko gaisuwa da qyar take amsa mata sauqinta d'aya saliha na zowa suyita fira abinsu snn duk zata je islamiyya Abba ke bata kud'in napep. Sae dai babbar matsalarta shine abinci wanda sae da kulawar Abba ake kawo mata abinci idan bai kula ba haka zasu barta da yunwa,mohd kuwa kmr ma baya garin don tun daga rnr bata qara ganin sa ba. Cikin shirin ta tsaf na islamiyya ta fito ta sami Abba zaune a falo ta durqusa har qasa ta gaida shi cike da ladabi ,ya amsa mata cikin sakin fuska tare da zaro dubu d'aya a aljihu zai bata ta girgiza kanta snn ta qara sadda kanta qasa tace"Abba ai kullum kud'in da kake bani sunyi yawa har ma ynx akwai canjin da zasu kaini yau da gobe, dad'i Abba yaji har ransa ba don komai ba sae don halayen Rynt dake matuqar birge shi,yace"to shike nn tashi ki tafi Allah yayi miki albarka" Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:18PM, 1/25/2017] Ummi Ya: 🔮```BAZAN BARSHI BA! ```🔮 _1/06/2017_ 🔮🔮🔮 _*page*_ ```20``` Zumbur umma ta miqe tace"haba Alhj! ni na d'auka ko zancen arziqi ne zanji ashe na tsiya ne.... Kina da hnkli shi zancen aure ne na tsiya...yo zancen tsiya man idan ba haka ba meye had'in mohd da wnn yrnyr er matsiyata er qauye ga 'ya'yan manya a gari,haba dan Allah! ,dan Allah Alhj ni ka ma daina wnn zancen. Baxan daina sa ba kuma aure tsakanin mohd da Rynt kmr anyi an gama ne, ai bake keda iko dani ba haka shima ba ajiye ni yayi ba da ko yaushe na masa zancen aure se yace tukuna sbd ya maida mutane en iska shasha.... Amma alhj tsakani fa da wnn cutar dashi kake sonyi ai gwanda ya zauna ba aure da ace wnn yrnyr ce matar sa sae kace bakin uwa a rasa wacce za'a ce ya aura sae ita haba dan Allah! Mtsw sae yau na fhmci rashin hnklinki ne kika yarfawa 'ya'yanki da kaf famlyn nn ba wanda yayi rashin mutuncin su ,na dai ji amma nikam sam bazan yarda da wnn zancen ba don wlh bazata sa6u ba wai bindiga a ruwa. Fuuu!Abba ya fita yana mai fad'in"tsakanin ni da ke sae aga wanda keda iko akan wani . Bai zarce koina ba sae downstairs ya samu still mohd na kan cin abinci yace da mohd idan ka kammala cin abincin ka same ni a d'aki. Nn take mohd ya kammala cin abincinsa yaje ga kiran Abba. Abba ya kalli mohd da ya nemi guri ya zauna a qasa yace"mohd ina son ka saurare ni da kyau kaji,kuma bana son kazo min da wani shashanci, zancen auren ka shin har yanzu baka sami wacce ta maka bane ko yaya? Aa Abba dama malika nake jira ta kammala karatun ta kuma ta kammala yanzu ni a shirye nake inshaAllh, Abba yayi shiru na tsawon lokaci can yace"er gidan wacece ita malika? ba wani bane Abba sananen mutum ne wato Alhj ilyas na Allah..... Alhj ilyas na Allah ,yace"eh Abba da wata matsala ne? Abba da yayi shiru yana mai nazari yace"Aa ba komai jeka" Cikin farin ciki mohd ya fito ya sami Rynt ta fito kenan tana neman shi. Yayi tsaye daga inda yake har ta qaraso gurin shi ,ba yabo ba fallasa ta miqa masa wyr tare da fad'in"ngde" snn ta juyo tayi ficewarta. Bayan kwana biyu da faruwar haka ne Abba ya sake kiran mohd. Yace"mohd a gsky zancen aurenka da wnn yrnyr malika sae dai nace kayi haquri sbd ba er mutunci bace kwata kwata shiyasa tun lokacin da ka snr dani waye mahaifinta na shiga nazari dmn nasha jin cewa baya ganin kowa da mutunci,sae gashi kuwa da mukaje hakane ta faru damu,dmn wasu banzan sharudda ya shiga snr damu kan auren ka da er sa wad'anda sam hnkli ba zai d'auka ba,don haka tunda ersa ba er gwal bace ka haqura da ita. Mohd da tun lokacin da Abba ya fara zancen sa yaji zufa na karyo masa. cikin rawar muryar yace"Abba malika yarinya ce mai mutunci kayi haquri kabar ni na aureta tunda ba cewa yayi bazai bada aurenta ba"Abba ya kalle sa kafin yake cewa "wae mohd ka koji irin maganganun da yake fad'a ne da kowanen mu sae da ya fito cikin 6acin rai wai ace hatta mahaifinku sa'eed da Allah yayi masa sanyin hali matuqa sae da yayi magana kan rashin mutuncin Alhj ilyas na Allah, gaskiya da sake don nikam baza ka kwaso min er gidan Alhj Ilyas na Allah ba ,koda kuwà ace ita kad'aice 'ya a duniya tofa sae dai ka hqr don baza ka aureta ba. Komai mohd bai iya cewa da mahaifinsa ba sbd gabad'aya lissafi ya kunce masa . Abba yace"gaka mohd ina wnn yrnyr Rynt er gidan inna? eh Abba ,to na yanke hukunci zan aura maka ita don wlh ta kwanta min arai kuma inaji a jikina ita alhairi ce a gare mu, cikin tsananin mamaki ya kalli Abbanshi yace"Abba wnn yrnyr fa kace" eh wnn d'in nn itafa Rynt ba.....ina Abba wlh ni bazan iya aurenta ba kawai dai ka bani dama wlh zan saisaita tsakanin ku da Abban malika, hm mohd kenan kaje dai kayi nazari akan aurenka da Rynt amma malika kam sae dai ka haqura da ita. Tashi ka bani guri! Da qyar mohd ya iya tashi ya bar gurin don gabad'aya jikin sa ya mace. Ya tafi 6angaren sa cike da tunani kala kala a ransa ya zauna kan sofa tare da dafe kansa ,can kmr wanda aka tsakura ya zari makullin motar sa ya fita. Wani katafaren gida ya nufa yayinda anguwar ta kasance very cylent ,ya parkar a bakin gate d'in gidan snn ya d'auko waya ya kira malika ,yana gama wyr ya d'aura kansa kan sitari ba jimawa sae gata ta fito cikin wani banzan dressing awa arniya ,kyau kam ba laifi akwaishi haka ma qirar jiki Alhmdlh kamar ita tayo kanta. Cikin isa da yanga ta shiga motar tare da fad'in "my man ya baka shiga ciki ba ka tsaya a nn kmr wani baqo? Mohd ya d'ago yana kallonta da idanuwansa da suka rine zuwa ja,yace cikin harsh voice"malika meyasa mahaifinki zai mana haka!"ta kauda fuskar ta gefe inda cikin sanyin murya tace"kayi hqr my man wlh nima banji dad'in abinda Abbana yayi ba,kasan hlin Abba sae a hnkli ,ba kace ga wanda yake mutunci dashi ba kowa ciwa mutunci yake..... Gud! ai gashi yanxu ya jamana baza mu auri juna ba ....ta zaro ido tare da fad'in "haba my man me yayi zafi haka? Sae da ya watsa mata mugun kallo kafin yake cewa"hln su iyayena duwtsu ne ko kuma basada zcy a qirji da Abbanki zai gaggaya musu maganganu ransu bai 6aci ba!,calm down my man sharudda ne fa ya kafa musu ba maganganu ya gaggaya musu ba,wane sharudda ne wai?tayi shiru tana kallon shi ,yace cikin d'aga murya "ki gaya min mana!kukan shagwa6a ta fashe masa dashi tace"nidai kayi haquri ba sae kaji ba wlh ba dad'in ji kuma don Allah ka ajiye zancen ba aure tsakanin mu wlh i cnt be wit a u, yace"malika ke da sauqi ma shin kinsan chakwakiyar da nake ciki ma ta had'ani aure da ake shirin yi da wata banza can er qauye ! A rikice tace"bangane ba"baza ki gane ba kam tunda mahafinki ya 6arar mana da lissafi. Ta wani marairai ce fuska tace"don Allah kamin bayani wlh ban fhmta ba"yace"malika Abbana ya hana min aurenki sbd zafin abinda Abbanki ya musu shine har yake qoqarin had'ani aure da wata kucaka,Komai kasa ce masa tayi sae kallon sa take hawaye na fmn zarya kan kumatun ta yace"take it easy don ko mutuwa nake bazan auri wnn yrnyr ba,abu d'aya nake so dake yanzu shine kisan yanda zakiyi Abbanki ya bawa iyayena haquri ya kuma janye banzayen sharuddansa to idan kika yi haka inshaAllah Abbana zai haqura. Share hawayenta tayi tare da fad'in"shikenan my man inshaAllah i will try my best" Kusan kwana hud'u amma malika ta rasa ta yanda zatayi ta shayo kan mahaifinta don ta sanshi kaifi d'aya ne in ya fad'i abu tofa shikenan. Mohd kuwa kullum bayada aiki sae na roqon Abbansa kan yayi haquri ya janye aurensa da Rynt amma sam yaqi . Rynt kuwa kwata kwata bata ma san da zancen ba ga soyayyar ta da munir sae abinda ya qaru wanda yanzu munir jiran dawowar inna kawai yake dmn ya snr da ita abinda ke tsakanin sa da Rynt ya kuma snr da ita yana so zai aure ta. Mohd ne durqushe a gaban iyayen shi kmr kullum yazo bada haquri a janye zancen aurensa da Rynt Abba yace"bafa zan janye ba idan har kaga na janye tofa lallai inna ce ta buqaci haka"haba Alhj gaskiyar magana kana son takura yaron nn ai kasan halin inna zama d'aya take amincewa da duk wani zancenka,kawai kar ma ka snr da ita zancen nn dan Allah ka bar yaron nn ya auri wacce yake so...na barshi ya auri wacce ya keso ai inace kinji abinda uban nata ya mana wae har mu yake cewa yaji ya amince zai bada er shi ga d'anmu amma fa mu sani shi er shi ba tunkiya bace ko akuya da zata je tana haifawa d'anmu 'ya'ya barkatai kmr yanda yake ganin a familyn mu ana haifo mana 'ya'ya hkn nn ba tsari,shi a tsarin sa bazai wuce ace ersa ta haifawa mohd 'ya'ya biyu ba idan ba haka ba tofa sae dai d'anmu ya haqura da ersa,wnn wace irin magana ce babu dad'in ji snn har kike tunanin zan amince na had'a surukuta dashi. To Alhj sae akace don ya fad'i tsarin sa shi zai sa dole abi ,muradi kawai ersa ta shigo hannun mu ,mu kuwa sae yanda mukayi da ita tunda ta rigada ta dawo a qarqashin ikon mu..... Sam bazan yarda da auren da za'ayi ana dinga ci min mutunci ba, dmn nida shi ba wanda zai nunawa wani kud'i ba kuwa zai zo yana dinga nuna min iko ba don kawai d'ana yana auren ersa! Cikin damuwa sosai mohd yace"don Allah Abba kayi haquri wlh a guna ba matsala ai yara biyun ma sun ishe mu jin dad'in rayuwa.....kul!na qara jin zancen nn ya fito a bakin ka!kuma maganata ta qarshe shine ba zan janye aurenka da Rynt ba wlh,sae idan ita Rynt d'ince ta furta da kanta cewa bata sonka, kuma ko bayan raina ban yafe maka ba idan ka auri malika! Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:18PM, 1/25/2017] Ummi Ya: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 ```Na Billy giro😊``` 5/1/2017 🔮```19```🔮 Cikin yanayi najin kunya tace"amin Abba ngde snn ta tashi ta fita ,Abba ya bita da kallo d'auke da murmushi a fskrsa. 6:15pm Rynt ce tsaye tana kallon rayuwar 'ya da mahaifi mai cike da ban sha'awa rayuwar su kmr rayuwar ta da Baffanta,a kullum sae ya rako ersa safe da yamma kuma idan aka tashi zata samu yazo yana jiran er tashi, da qafa suke zowa kuma da qafa suke komawa sbd ba wani jayawa da inda yake fitowa,sak yrnyr zata iya maida kanta gida amma so irin na 'ya da mahaifi kesa kullum yake zowa d'aukar er shi,hkn ba qaramin tuna mata rayuwarta da baffanta suke yi ba,sbd itama haka Baffanta ke mata a lokacin da take primary mkrntr ba wani nisa da gidansu amma kullum baffanta sae ya rakata haka kuma duk aka tashi zata samu yazo yana jiranta su koma gida. Baffa shine sunan da yrnyr ke kiran Abbanta dashi hkn ke dawo ma Rynt da ryuwar ta sabuwa fil,shiyasa kullum bata da aiki sae na kuka idan tana kallon rayuwar su. Ko yanzu hawaye ne suka silalo a hnkli kan kumatunta ta kai hnnu a cikin niqab d'inta ta share hawayen yayinda take magana a ranta cewa _"Bazan yafe maka ba ba kuma zan ta6a barin ka ba, ka yanke min farin cikin rayuwata haka nima zanyi silar yanke taka"_ "Rynt"cewar munir wanda yazo gab da ita ya tsaya har tana jiyo qamshin turaren shi, bata kalle sa ba sbd lokacin wasu hawaye ne ke faman zarya kan kumatun ta,duk da cewa da niqabi sanye a fuskarta sae take ganin kmr zai iya hangowa idan ta kalle shi. A hakan ta gaida shi ya amsa yana mai kallon gefen da take kallo wato 'ya da mahaifi da sukayi er nisa a tafiyar su, ya nisa tare da fad'in"dama na jima ina son nayi miki wata tamvaya Rynt, meyasa kullum sae na ganki kina kallon mutanen nn shin kin san su ne? Cikin sanyin murya tace"ko d'aya haka kawai suke bani sha'wa" Gama fad'ar hk takai hannu zata tsaida napep yayi saurin dakatar da ita ta hnyr cewa"dan Allah Rynt yau ki barni na kaiki gida kinji"Aa wlh ka barashi kawai ngde"pls Rynt baki san yanda nakeji ba wlh sam bana son ganin kina shiga napep bayan ni inada abinda zan riqa kaiki gida"um um nidai ka barshi nagode" daga hk ta shige napep ta barshi. Tana isa gida ta samu sae lokacin malamin su saliha ya tashe su sbd su a cikin gida ake karantar dasu. Sae da ta d'an gyra fuskarta sbd har lokacin kuka take,snn ta cire niqab sae kawai sukayi ido hud'u da malamin su saliha zai fita,ga mamakinta kallonta yake har sae da ta gaishe shi snn ya kauda idonsa,ta maida dubanta gun saliha wacce ta qaraso gurinta sake da fuska Rynt tace"wae ku sae yanzu aka tashe ku?eh wlh kedai makara yayi bai zo da wuri ba,Rynt tace"wae nikam meyasa Abba bazai barku ku riqa zuwa isalimiyya ba don kmr hkn zai fi..... Mtsw!Ameera da ta biyo zata wuce taja wani dogon tsaki tana mai hararar Rynt kmr idanuwanta zasu fad'o tace"to wacce ta san dai dai ai sae kije da kanki ki snr da Abban namu abinda yake dai dai tunda shi bai sani ba, banxa er qauye mai banzar rayuwa!mtsw ta koma jan wani tsaki ta wuce. Ita dai Rynt kallonta kawai tayi saliha tace"don Allah kiyi haquri haka hln Ameera yake kowa bata gani da gashi,murmushi Rynt tayi snn tace"nikam ko kad'an banji zafi ba wlh,nn dai saliha ta qara bata haquri snn kowa ta kama gabanta. Rynt na shiga ciki ta had'u da Abba ya fito zai tafi masallaci tayi saurin durqusawa har qasa ta gaida shi, fuskar sa wasae ya amsa mata snn yace"Rynt an dawo daga islamiya? Can murya qasa mai d'auke da tsantsar ladabi tace"eh Abba" yace"to Allah taimaka tashi ki shiga daga ciki kiyi sallah ki kuma sami abinda kika ci kafin dinner kinji"tace "to Abba" snn ta tashi ta wuce shi kuma ya wuce masallaci. Yau satin inna d'aya da zuwa qauye. A washe garin rnr ba islamiya sbd rnr alhamis ce Rynt ta shiga cikin en aikin gidan tana taya su aiki. Abba ne ya fito ya same ta tana goge kan dining tana ganinsa ta durqusa ta gaida shi ya amsa Yana mai kallon yanda idanuwanta suka kumbura yace"lfy Rynt me ya sami idanuwanki? Sadda kanta qasa tayi don dai baza ta iya cemai kuka tayi ba,sae dai ta gaya mai abinda tayi bayan kukan tace"Abba kwana nayi ina karatu" Hln kun kusa fara jarabawa ne?Aa hardar qur'ani nakeyi, Abba ya jinjina kansa snn yace"haqiqa kinyi dabara Allah ya qara miki kaifin baseera" cikin sanyin murya tace"amin Abba nagode" Yace "to ya naga kina aiki saki akayi ?Aa ina taya su ne kawai,to idan dai kinji kin gaji kar ki tilasta kanki ga qarasa aikin ki komawar ki kiyi zamanki kinji. Gyad'a masa kai tayi yayinda ya ciro wyrsa a aljihu dake faman ruri ya d'aga ya tafi,Rnyt kuwa taci gaba da nata aiki. umma ce a d'aki ita da Ameera yayinda umma ke matsawa Ameera kan ta tashi taje ta gyarawa mohd 6angarensa sbd yau zai dawo,cikin kukan shagwa6a tace"wlh umma kinsan halin yaya duk yanda aka gyra masa guri sae yayi fad'a wae bai yi ba, au kinsan dai baya son en aiki su gyra masa d'aki ko,ko kuma ni kike son naje na gyara masa? Aa umma ga wnn yrnyr mana mai baqin son aiki tana can yanzu haka tana taya su sahura aiki, don Allah umma kice taje ta gyara masa, to shikenan naji jeki snr da ita ki kuma nuna mata 6angaren snn ki dawo. Sosai 6angaren ya matuqar birge Rynt har ganin take kaf gidan ba inda yakai 6angaren mohd kyau . Sae da ta gama qauyancinta snn ta gyra dak'in tsaf har bathroom ta kuma feshe d'akin da room fresh kala kala da ta samu kan dressing mirro d'insa. Bayan tayi wanka taci abinci ta tafi 6angaren su saliha ta sami umman saliha zaune a falo saliha na cire mata qumba, ta gaishe ta cikin ladabi yayinda mamar ta amsa cikin sakin fuska har tana cewa"er halak kmr kinsan zancen ki muke ina fad'in yau dai shiru saliha bata je ba baki shigo ba, Rynt tai murmushi tace"wlh mama na d'anyi wani aiki ne" to sannu ,zaki iya zuwa kasuwa yau kuwa saliha ce ta matsa min wae tana son ku siyo inner wears da kayan kwalliya nace ta bari na bayar a siyo muku tace ita tafi son kuje da kanku, ta gefen ido Rynt ke kallon saliha dake faman roqonta kan tace eh, dako d'an murmushinta tace"eh mama xan iya" To shike nn kuje ku rubuto duk abinda kuke so se kuxo na baku kud'i...a'a mama ki bamu kud'i kawai in munje zamu ga abinda muke so ai, Aa saliha nafi son ku rubuta sae na baku kud'in enuf, amma fa kar a manta da er autata ita ma a siyo mata nata, "to shike nn mama ai baza mu manta ta ta ba"nn taja hannun Rynt tace "muje ko" Bayan sun shiga ne saliha ke cewa"Rynt ni kuwa wane aiki ne kikayi da duk yawan en aikin gidan baza suyi ba sae ke?hm na gyarawa yayanku d'akinsa ne wae zai dawo....cabd'i Allah ya cece ki da masifar sa, Rynt ta zaro ido tace"me?saliha tace "ba wani abu bane fa shidai matsalar sa d'aya duk yanda aka gyara masa d'aki sae yace bai yi ba yayita masifa kuwa. Hm ni ba masifar sa ba ma ,zagin da yake yi ne bana so don wlh na tsani a zagar min uba ,"shi kuma yanada wnn" cewar saliha snn tace" sae dai kiyi haquri don muma wlh haka yake zagin mu in ya tashi masifar sa. Cikin muryar kuka Rynt tace"Ai gwanda ku naku iyayen suna raye ba zafi kmr ni da basa raye" Saliha tace "haba Rynt meye na kuka kuma "Baffa"cewar Rynt wacce ta rungume saliha tana kuka tace"saliha wlh ina mutuwar son baffana amma an raba ni dashi zama d'aya, ba a barni da zafin ba ana kuma zagar min shi" Saliha tace"kiyi haquri Rynt haka mutuwa take bata barin wani don wani.... _shiyasa nima Bazan bar wanda ya kashe min shi ba koshi waye_ Haka Rynt ta fad'a a ranta yayinda saliha taci gaba da cewa"shi kuma yaya dake zagin ki ai kansa ya zaga ba kowa ba" Nn ta samu ta rarrashe ta har ta daina kuka,snn ta rubuta abinda suke so ta kaiwa mama ta basu kud'i suka tafi kasuwa. Guraren qarfe 3 mohd ya dawo shi kad'ai ba tare da kowa ba. 6angaren sa ya nufa yana bud'e 6angaren wani qamshin dad'i ya daki hancinsa ya kuma ga komai tas tas very neat ba kmr yanda ake gyra masa d'aki ba, dmn har bathroom ya duba bai ga matsalar komai ba sae ma wani qyalli da yake , ya fito ya durqusa tare da d'ora d'an yatsansa akan tiles ya shafo ba wani datti, har ransa yaji dad'in gyaran ya kuma qudiri kyauta ga wanda yayi gyaran,don yauce rnr farko da ya ta6a samun d'akin sa hundred percent . Sae bayan qarfe hud'u su Rynt suka shigo 6angaren su Ameera wad'an da dama tuni sun dawo da kasuwa suna can 6angaren su saliha zamansu. Mohd suka samu jingine a jikin motar sa yana waya wanda kallo d'aya zaka yi masa kasan da masoyiyar sa yake waya. Gaida shi sukayi ya d'aga musu hannu kawai, bayan sun d'an wuce saliha ke cewa"waeh!na miki murna kin huta da bala'in sa yau" Cikin rashin fahimta Rynt tace" ko meyasa"sbd yana waya ne da masoyiyar sa Anti malika da yake mutuwar so,wacce baya samun suyi waya kullum sbd aikinsa da kuma yanayin karatun ta shiyasa duk rnr da yayi waya da ita tofa bazai yi masifa a rnr ba,,Rynt ta girgiza kanta tare da fad'in"hm mugun gaye ashe yana soyayya har wae ma kuka sani" tayi mgnr ne a ranta ashe ta fito Har Saliha ke cewa"wa! ai ba wanda ya sani koni qanwarta qawata ce sosai a school shiyasa na san komai,dmn ma akanta yayi tafiyar nn zuwa UK don tayata murnar kammala karatun ta shine ya jirata suka dawo tare wanda inshaAllah mun kusa shan biki sbd tuni ita yake jira. "Yayi Allah taimaka" cewar Rynt kafin take cewa _"abin tausayi malika rnr aure mijinki gawa"_ Basu jima da shiga ba mohd ya shigo ya sami Ameera na saukowa ta fito daga d'akin umma yace"ke wa ya gyra min 6angarena "cikin inna inna na jin tsoron sa tace"bani bace wlh wnn yrnyr ce Rynt" je kiramin ita" ta tafi sae dad'i take ji yau kam fad'an bazai qare kanta ba. Rynt ta fito sanye da qaton hijab d'inta har qasa , ta same shi zaune kan dining har ya fara cin abinci. Taje kawai tayi masa tsaye tare da kauda kanta gefe ,ya d'ago fuskar sa a hnkli yana kallonta snn yace"kece kika gyra min d'akina wae?a taqaice tace"eh" Ya ta6e baki yace"hm abun mamaki a qauyen naku ke ke gyarawa sarkin garin ku d'aki ne?eh har ma da sarkin kd duk ni ke gyara musu d'aki,da sauri ya kalleta sbd su asalin en kd ne yasan agun inna taji, baqa ta masa kenan,yace"ke ina wasa dake ne? um um kaidai ka nemi na maka haka amma ni ba halina bane raina wanda ya kama girmansa,d'an fari da ido yayi sae kuma yayi murmushi yace"to naji a wuce gun ga wnn ladan gyara min 6angare na da kikayi,Rynt ta kalli kud'in da ya ajiye gabanta zasuyi 20k tace"nayi dan Allah ne ba don wani abu ba" Eh na sani ai kyauta ce na baki.... Kyautar ce bana so ,ya d'ago da d'an mamakinsa sae kuma ya basar yace"to me kike so? Har tayi niyyar saka mai wata maganar sae kuma ta fasa ,tace"waya nake son nayi da inna" Ga mamakinta sae ya ciro waya a aljihunsa ya kira mata inna ya bata, bata san lokacinda murmushi ya su6uce mata ba ta kar6i wyr ta kwasa da gudu zuwa d'aki, mohd kuwa binta yayi da shu'umin murushi yayinda a ransa yake mamakin raina sa da tayi. Duk abin nn da suke Abba na kallon su sae ya musu wata fahimta ta daban wacce tasa yaji dad'i har ransa, da saukowa zai yi amma ya fasa ya juya zuwa d'akin umma , ganin yanda yake murmushi yasa ita ma ta shiga murmushi tace"yadai Alhj? Sai da ya zauna snn yace"zauna tukun" nn kusa dashi ta xauna. Yayi gyran murya snn ya fara da cewa" haqiqa tun zuwan Rynt a gidan nn na yaba da hnklnta da kuma natsuwarta har hakan yasa na kwad'aitu da son ace ta zamo cikin wnn family namu ma'ana ta kasance suruka a gidan nn mata ga mohd. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:18PM, 1/25/2017] Ummi Ya: 🔮```BAZAN BARSHI BA! ```🔮 🔮🔮🔮 _*page*_ ```21``` Amma Alhj Allah ya isa tsakanin mu dakai don wnn cutuwa ce wlh! Cikin nuna fushi Abba ya nuna ta da yatsa yace"wlh Rabi'a ki kiyaye ni da banzan kalaman nn naki dake shirin janyo miki mutuwar aurenki! Gama fad'ar haka ya tafi kmr wanda zai tashi sama. Umma kuwà ta bishi da kallo ta6e da baki tace"indai wnn kalmar ce ba yau na saba jinta a bakinka ba bare ta tayar min da hnkli,snn ta kalli mohd da ya shiga cikin tsañanin tashin hnkli tace"kaga kwantar da hnklinka aurenka da malika kmr anyi an gama kuma baza ka auri wnn er qauyen ba indai ina numfashi a doron qasa,kmr wanda zai yi kuka yace"umma ta yaya kike ganin hkn zai yiyu bayan kinaji Abba rantsuwaa yayi kawai ma umma dan Allah ki daina sa bakin ki a zancen nn sbd ko kad'an banji dad'in yanda Abba ya sako rabuwar aure a zancen nn ba .... Yo ai ba yau ya fara ba kuma dan ya rantse sae me! Kaidai tashi ka tafi kawai ai er iskar yrnyr zata dawo daga islamiyya ta sameni.....Aa ki barni da ita kawai umma ni nasan yanda zanyi da ita....ai da ka barni da ita wlh...No umma bana son kwata kwata wani abu ya had'aki da ita ne bare ta raina ki. 6:00pm Rynt ce tafe kan hnyr dawowa islamiyya ita da munir sae er fira suke mai cike da nishad'i yayinda Rynt ke d'an duba kan titi ko zata hango napep. Kmr daga sama ta hango motar man tafe ya zo gab dasu ya tsaya kmr mai shirin taka musu qafafu don tsirif ya rage har sae da sukayi saurin ja da baya. Dukkan su da mugun kallo ya fito yana binsu dashi,yace da Rynt shiga mota"kallon sa ta tsaya yayi ya daka mata tsawa yace"shiga mota nace!cikin 6acin rai taje ta shiga motar ya zagaya ya shiga yaja motar a tsiyace had'e da bazawa munir qura. Tafiya yayi da ita mai nisa snn ya samu guri ya parker ya kalli Rynt da tun lokacinda yaja motar gabanta ke dukan tara tara kaddai ace ya gane ko ita wace ce,yace"oya cire wnn baqin abun dake kan fuskar ki magana nake son zanyi dake" Ba musu ta yaye niqab d'inta ba tare da ta kalle sa ba. Sae da yakai hannu ya d'ago fuskarta yana kallonta shaye da toka snn yace"abu zan nema agunki wanda ban ta6a nema agun kowa ba wato alfarma, alfarmar itace ina son dan Allah idan Abbana ya kiraki ya tambaye ki ko kina sona kice masa A'a shine kawai ni kuma idan kika min haka nayi miki alqawarin duk wani abu da kike so a rayuwa ki tambaye ni zan miki shi koma mene ne kuwa"amma wlh kar ganin na had'aki da Allah ki raina min da wayo dmn duk kika yi gigin amincewa buqatar Abbana sae dai a nemi wata bake ba! Manyan idanuwanta farare tas take ci gaba da kallon shi dasu snn ta ta6e baki tace"ai sae ka fayyace min komai ta yanda zan fhmta" Mugun kallo ya watsa mata yace"daqiqiyar inace ke da bazaki fhmta ba ,da Allah ni ftr min daga mota kuma wlh ki tabbatar kinyi abinda na saki! Ba musu kuwa ta fita motar don yanda taga yanayinsa ko tura ta zai iya yi ta fad'i, sae dai da gani akwai mgnr da takeyi a ranta haka kuma akwai nazarin da takeyi shi kuma mohd har lokacin kallon takaici yake mata snn yaja motarsa a tsiyace ya bar gurin. Da qyar Rynt taga ta sami napep sbd yanayin anguwar da ba kwaramniya bare abin hawa ya yawaita. Nazari take yi kam har ta isa gida ko kuma nace har akayi sllr isha'i bata daina nazarin ba yayinda tuni zuciyarta ta ganar da ita abinda ke shirin faruwa sae dai taqi bawa kanta damar amincewa da hkn har sae Abba ya kirata tukun taji koma mene ne. Tana gama cin abinci Abba ya aiko Ameera yana son ganin ta. Taje ta same shi shi kadai zaune a falo. Ta nemi guri a qasa ta zauna ta kuma gaida shi cikin ladabi kmr koyaushe. Cikin sakin fuska ya amsa snn yayi gyran murya yace"Rynt haqiqa duk mutumin da ya zauna dake zai yi sha'awar kyawawan halayenki da kuma d'abiunki,a dalilin hakane ma yasa nayi sha'awar had'aki aure da mohd,amma kuma ba dole sae idan kina ra'ayi kuma dan Allah kar ki 6oye komai a ranki,dmn ita rayuwar aure wata sabuwar rayuwace da ta banbanta da kowace rayuwa wacce dad'inta ka auri wanda kake so yake sonka, shiyasa nake son ki snr dani gskyr abinda ke ranki ma'ana idan ba kya ra'ayin auren ki da mohd kar kiji shayin komai ki snr dani idan kuma kina ra'ayi sae dai nace Alhmdh dmn zanfi kowa farin ciki da haka. Tun farkon fara zancen sa ba qaramin girgiza Rynt tayi da jin zancen ba amma sae ta dake bata yarda ya fhmci halinda take ciki ba. Bata son mohd bata kuma jin zata soshi har abada!amma kuma ko don ta d'auki fansarta a sauqaqe zaisa ta amince da aurensa to kuma ya zata ce da yaya munir dake matuqar son ya aureta. Duk a cikin ranta take wnn tunanin ,Abba ya katse ta da cewa ke nake saurare Rynt ,sae da ta qara sadda kanta qasa snn tace"na Amince Abba zan aure shi"Abba yace "kin tabbatar Rynt ba cutar kanki kikayi ba? eh wlh Abba har raina na amince. Wani irin dad'i Abba yaji har ransa, yace"Allah yayi miki albarka Rynt, ya kuma sa ki gama lfy da duniya"da qyar ta iya cewa amin kan kukan da ke qoqarin zo mata sbd tuna baffanta da tayi da kusan kullum sae yayi mata irin addu'ar nn. Koda ta koma d'aki ba kowa sae tayi kwance abinta tana ta kukan tuna Baffanta har sae da tayi mai isarta snn ta tashi tana tunanin me zai faru idan mohd yaji ta amince da buqatar abbanshi ko ita ma kasheta zai yi kmr yanda ya kashe mata Abbanta. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:18PM, 1/25/2017] Ummi Ya: [ 1/8/2017] 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 🔮🔮🔮 _*page*_ *```22```* Don tasan a rashin imaninsa zai iya aiwatar da abinda ma yafi haka in akwai, amma kuma bari taga shin me yake nufi da sae dai wata ba ita ba. Abba kuwa da mohd har umma ba wanda ya kira cikin su bare ya snr dasu yanda sukayi shi da Rynt kawai ya yanke hukunci sae inna ta dawo su yanke shawara shi da ita asa rnr aure. washe gari hnklinta a kwance tayi shirinta na islamiyya ta fita. Ko minti 5 batayi da fita ba inna ta dawo daga qauye kuma a nn gidan ta sauka sae murna ake da dawowar ta yayinda ita kuma ta matsu taga Rynt nn Abba ke snr da ita ai ta tafi islamiyya. Bayan inna taci abinci ta d'an huta Abba ya shiga snr da ita shawarar da ya yanke kan zancen had'a mohd aure da Rynt har yanda sukayi da Abban malika duk sae da ya snr da ita. Sosai inna tayi murna ba kad'an ba haka kuma itama bata bada goyon bayan mohd ya auri malika ba wanda duk zancen nn da suke yana kunnen hjyrsu mohd wacce tana gama sauraren kaf abinda suka tsara ta koma d'aki cike da masifa ta kira mohd a waya ta snr dashi tace"ga irinta nn sae da nace kbr ni da yarinyar nn ni nasan yanda zanyi da ita wanda ko da kuskure baza ta yarda ta amince da zancen Abbanka ba wlh, amma kace a'a wae kar ta rainani ,raini duk ya wuce ace kmrta baqauya er matsiyata ta had'a surukuta dani,mohd yace"yanzu umma kina nufin duk yanda nayi da ita ta amince da buqatar Abba? Hm!na nawa kuma gashi har sun tsara anjima da dare iyayenka zasu tafi gidan inna asa ranar aurenku!ai wlh kayi wa kanka!don yanzu sae kasan yanda zakayi ka ftr da kanka ko kuma ka nemi wata uwar don muddin ka rasa mafita har takai ga an aura ma ita tofa bani ba kai tunda tun farko sae da nace kabarni da ita kaqi. Daga haka ta katse wayar sae huci take tace"in shi mai hnkli ne ko islamiyya baxata dawo ba sae dai wata ba ita ba amma bari nasa ido naga ko dabara ta tayi!in yaso ni kuma na tayasa da wani aikin ta yanda baza ace dasa hannun mu kan 6acewar ta ba. Mohd kuwa hjyrsa na kashe waya ya rasa ta inda zai sa kansa kan baqin ciki da kuma tunanin hukuncin da zai yiwa Rynt. Ya zama dole yaje ya jirata kan hnyrsu ta islamiya don yau sae ta fad'i wanda ya aiketa . Yana fita da motar sa yayi kici6is da Malika ta parker motar ta ta fito, dole ya tsaida tasa motar ya fito yaje gab da ita ya tsaya yana mata wani irin kallo,ita kuwa ta wani langwa6ar da kanta snn tace"my man wai ya ake ciki ne tun jiya da mukayi waya naji shiru har yau " yace"to shine zaki wani biyo ni har gida da kuma wnn banzan dressing d'inki salon Abbana ya ganki yace bakida kamun kai kuma,in yaso Komai ya qara cakud'e mana! Kayi haquri my man wlh banda wasu kaya sae ire iren su kuma ka sani,to me ya hana ki kirani a waya muyi magana? Ina mgnr zata yiyu a waya nida kwata kwata daren jiya ban samu nayi bacci ba,amma malika kinsan bana son damuwa koma mene ne ai zanje na sameki har gida,kayi haquri na damu ne sosai ,tayi mgnr cike da qwallah tap a idonta, yayi saurin cewa"shikenan kar kiyi kuka gaya min me kike so yanzu?so nake ka gaya min abinda ake ciki ,ajiyar zuciya ya sauke snn yace"wnn yrnyr ta lalata mana komai don ta amince da buqatar Abba snn kuma Abbana har yanzu dai yana kan bakarsa na bazan aureki ba,amma kar ki damu zan shawo kan matsalar komai inshaAllah ,matsalata d'aya yanzu shine anjima za'a sa rnr aurena da wnn yrnr shiyasa at all kaina ya kunce bansan ma wane hukunci zan yanke ba, ga umma ta sani cikin wata chakwakiyar wae bani ba ita idan ban nemo mafita ba har akayi aurena da wnn yrnyr.... Wae da kana nufin zaka yarda ayi auren ne to! Malika uba ba abin wasa bane idan kuma ya yanke hukunci ba yanda za'ayi kuma ya rantse cewa in ta amince tofa shikenan ba fashi aurena da ita, but my man be wise mana,idan ba yrnyr ai ba auren shike nn dole Abba ya haqura, aikin hnkli dai malika ina mai gaya miki 6atar wnn yrnyr tmkr tsinuwace na jawa kaina don dole Abba yasan nine, kawai dai zan aureta amma na d'an wani lokaci .....Wlh! my man bari kaji in gaya ma ba maccen da ta isa ta aure ka bayan ni don ka ma daina wnn sa6on!daga haka taja motar ta a tsiyace ta bar gurin. Har zai shiga mota sae ga kiran Abba yana son ganin shi,dole ya juya ya tafi ga kiran Abba. Yau Rynt ita kad'aice kan hnyr dawowa islamiya sbd da safe munir bai cika zowa ba sae da yamma. Tana cikin tafiyar ta har takai titi zata tsaida napep sae ga wata tsaleliyar mota ta tsaya a gabanta. Malika ce ta fito daga motar taje gab da Rynt tare da kai hannu ta yaye mata niqabi,nn malika ta yamutse fuska kmr wacce taga kashi tace"hm rainin wayo wai kece ke shirin shiga tsakani na da my man,ta nuna ta da yatsa snn taci gaba da cewa" lemmi tell u 1 thing ruwa ba sa'ar kwando bane haka kuma ramin kura ba gurin shigar akuya bane,a bisa yanda ma na fhmta kwata kwata tsabar talauci ne ke d'ibar ki da haka zan taimaka miki na baki check ki rubuta duk iya kud'in da kike so after that ki sani inda dare ya miki ma'ana kwata kwata ki 6acewa duniyar mu ki tafi can taku duniyar ta matsiyata wnn umarni ne dmn in kika sake kika dawo gare mu wlh sunanki gawa! gama fad'ar haka ta zaro cheque da biro ta miqawa Rynt ,sae kuma tace "koda yake nasan duhun kai na tattare dake bare har ki iya rubuta wani abu nn ta rubuta million biyar snn ta ce ungo kud'i ne masu yawan gaske da nsn ko ubanki bai ta6a riqa irin su ba bare ke! Kallonta kawai Rynt keyi wacce batada niyar kai hannu bare har ta kar6i cheque d'in . Malika tace"gwanda ki kar6a don wlh kanki kika yiwa idan baki kar6a ba sbd ynzu hk ni a shirye nake da nasa a yanke miki hukuncin da yake dai dai a guna. Komai Rynt bata ce mata ba sae ma ra6awa tayi ta gefenta zata wuce ,sae kawai ta sami kanta da ganin qarti zagaye da ita. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:18PM, 1/25/2017] Ummi Ya: [ 1/9/2017] 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 🔮🔮🔮 _*page*_ *```23```* wayar malika ce tayi qara koda ta duba Man ne mai kiran, ta d'aga wyr sae jin tayi yace"malika kibar er mutane ta wuce" tace "my man.... sae taga ya katse kiran. Kallon mutanen ta tayi tace"ku barta ta tafi. Bayan Rynt ta wuce suma mutanen nata ta basu izinin wucewa snn ta shiga rarraba ido ta inda zata hango man dmn tasan tabbas yana gurin. Kmr daga sama tana juyawa ta ganshi a bayanta kallonta yake da mamakin yanda akayi tasan Rynt har tasan makarantar su sae kuma nn take ya basar sbd sanin bincike ba abinda baiyi yace"daso kikayi mahaifina ya tsine min ko kuwa?my man.....No kawai kar ki sake min shisshigi irin wnn bana so! Daga hk yayi tafiyar sa ya barta. Hjyr su pretty kuwa sae sa ido take taga ko Rynt zata dawo amma shiru haka Man bai dawo gidan ba. Wasa wasa kuwa har yamma ba Rynt ba labarinta, dad'i taji sosai har ranta don ganin take dabarar tace tayi. Taja Ameera zuwa d'aki wae ta rubuta takarda a cewar Rynt ce ta rubuta ta yanda idan Abba ya gani ba zai zarge su ba haka kuma ba zaisa neman Rynt ba. umma ce ke fad'in abinda za'a sa Ameera na rubutawa har suka gama tace "yi maza kije kisa a qarqashin pillown ta kina jin shigowar Abbanku kije masa cikin kuka a cewar kin nemi duk gwalgwalanki ki ransa har ma kud'in provision dinki da ya baki jiya da dare ni kuma zan fito da nawa tuggun ta yanda koshi waye bai isa ya gane plan bane wlh,yi maza jeki........ Ameera!Ameera! kiran ya fito daga Abba umma tayi saurin kar6ar takardar dake hannun Ameera ta tura mata cikin zane,nn suka ji knocking umma ta bud'e qofa Abba ya kalli Ameera yace"ke je ki ftr da kayan Rynt za'a maida su gidan inna ne, umma tace"ina ita Rynt d'in da baza ta ftr ba sae Ameera? Da mamaki Abba yace"ai Rynt bata dawo gidan nn ba tun safe sbd ana tashi daga makaranta inna ta aika Nasir ya d'auko ta, yanxu haka ma tana gidan inna har ma taje islamiyyar yamma ta dawo. wani irin baqin ciki umma taji tace"ai sae tazo da kanta ta ftr da kayan tunda Ameera ba boyar gidansu bace"tsawa ya dakawa Ameera yace "ke je ftr min da kayan Rynt nace" Ameera ta wuce kmr xata yi kuka,ya kalli umma yace"keda kanki wae kike lalata rayuwr 'ya'yanki Allah dai ya shirye ki". Abba ya fita ya bar umma cikin takaici da jin haushin mohd. 7:00pm Mohd ne ya shigo gidan inna,inna ta fito daga kitchen kenan tana ganin mohd ta washe baki tace"ka ganmu muna can nida baaba hurera da Rynh muna had'awa iyayenka liyafar da xasu ci idan sunxo sa rnr aurenku kaida Rynh. Kauda kansa gefe yayi dan shi ko sunan Rynt baya son ji. Inna tace"akawo maka naka abinci? Aa inna magana nazo muyi, inna ta washe baki tace"ayyo to bari na kira ma Rynh d'in"ransa ne ya qara 6aci yace"na mata me ni dake zanyi magana" Washe da baki inna ta nemi guri ta zauna shima haka tace "ina jinka maigidana angon Rynh" Ba yanda ya iya hk ya dake ya basar awa bai ji ta ba yace "inna so nake dan Allah ki roqa min Abba ya barni na auri malika.... Inna ta fiddo ido waje tace"yau naga shashashan yaro ita Rynh d'in fa? Ai inna ba ina nufin wani abu a kanta ba kawai dai so nake Abba ya barni harda malika d'in na had'a na aura sbd gsky ni ita ce za6ina.... To bakaji da kyau ba wnn er marasa mutunci tayi kad'an ta shigo cikin dangin mu ta watsa mana mugun iri,dan Allah inna ki saurare ni fad'in ra'ayin Abbanta ba shine rashin mutunci ba ai ,kaga mohd indai wnn maganar ce zaka tamin gwanda ka tashi kayi tafiyarka don ba saurarar ka zanyi ba,cikin damuwa sosai yake kallon inna kmr zai mata kuka yace"inna wae dan Allah meye dad'in aure ba ka auri wanda kake so yake sonka ba... Yo mu kenan duk kana nufin ba muji dad'in aure ba muda duk had'in iyayene amma muke zaune qalau har Allah ya d'auki ran marigayi,amma inna daa da yanzu ba d'aya bane kin sani...ina ko zasu zama d'aya tunda daa iyaye ke za6awar 'ya'yansu mata kuma ba'a jin kansu amma kai yanzu gashi kazo min da zancen za6in ka kake son ka aura mu daa har akwai wani za6i da ya wuce na iyaye. Nidai inna kiyi haquri ki roqa min Abba kafin su shiga meeting d'in nn....yo kana nufin za'a had'a baki dani ne a cuci Rynh ,haba inna aini ake shirin cuta shin ba kya jin tausayi nane a matsayina na jikan ki ace duk tsawon shekarunda na d'auka a matsayina na lafiyayye banyi aure ba ina nn ina jiran malika ta kammala karatu se kuma ace bazan aureta ba,fisabilillah inna ya kamata a duba min,ya qarashe mgnr ne ta yanda duk wanda ke saurarensa dole ya tausaya masa,inna ta sauke ajiyar zcy tace"shikenan mohammadu zanyi magana da mahafin naka amma idan bai amince ba tofa sae dai ka haqura don bazan tilasta masa ba. Ba komai inna nagode ya tashi zai fita tace"abincin ka fa? sae anjima idan na dawo, to a dawo fly. Daga haka ya fita ita kuma ta koma kitchen. Sae tara da rabi mohd ya dawo gidan ya samu Abba a nn falo shida inna sauran iyaye kuwa an kammala meeting d'in sun tafi. Cike da ladabi ya gaida Abbanshi ya juya zai fita Abba yace"zauna dama kai nake jira muyi magana. Bayan ya zauna Abba ke cewa naji na kuma amince da buqatar ka amma fa ka sani ya zama dole kayi adalci a tsakanin su snn bayan aure idan term ya zagayo zaka saka Rynt a makaranta yayinda nauyin karatun ta zai kasance a qarqashin ka. Abinda ya rage yanzu shine ka snr da iyayen malika zancen auren naku wanda za'a d'aura a qarshen wnn satin rnr juma'a idan kuma basu shiryi hakan ba su suka sani don baza a fasa naka dana Rynt ba. Daga haka Abba ya tashi ya fita mohd ya d'ago ya kalli inna tare da fad'in nagode inna. Yana fita gidan inna bai zarce koina ba sae gidan su malika ya snr da ita Abban sa ya amince suyi aure amma cikin satin nn za'ayi komai dad'i taji sosai har da su hugging d'inshi wacce kwata kwata bai nuna mata still auren Rynh na kanshi ba,ita kuwa ta d'auka an fita zancen Rynt. Sae shirye shirye ake tayi a cikin satin har ma ya zamo inna ta hana Rynt fita ko ina wae ta shiga lalle kenan saliha kuwa tarewa ma tayi a gidan, Rynt kuwa sae kallon su take tana tunanin hln da munir zai shiga idan yaji. 6angaren hjyr mohd kuwa tun daga rnr ko gaisuwar mohd bata amsawa wae a cewar fushi take dashi tunda yaqi neman mafita duk da cewa wani 6angaren taji dad'i jin cewa harda malika zai aura. Rnr juma'a aka d'aura aure akayi walima 6angaren su malika kam shagugula akayi ba kad'an ba. Da dare za'a kai Rynt sae kuka take kan rabuwa da inna haka ma inna kukan take kmr baza su qara had'uwa ba. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:18PM, 1/25/2017] Ummi Ya: [ 1/10/2017] 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 🔮🔮🔮 _*page*_ *```24```* Bayan ankaita kowa ya watse ita kad'ai a d'aki sae autar su saliha da suke kira da mami. Ambar mata ita ne sbd ita Rynh d'in ta nemi haka sbd mugun tsoron bacci ita kad'ai take ji. 6angaren su mohd kuwa bayan an kawo amarya suka tsiri wani party maxa da mata sae shagali suke duk Rynt ta kasa samun baccin kirki sbd hayaniyar su hkn yasa ta tashi ta d'auro arwala ta shiga yin nafilfili yayinda autar mama keta sharar baccinta. Sae kusan qarfe d'aya da rabi en party suka watse amma hkn bai hana mohd da malika suka sha amarcin su ba. Washe gari sae da Rynt tayiwa mami wanka snn ita ma tayi nata wnkn. Ta gama shiri kenan taji an turo qofa saliha ta shigo mami taje da gudu ta rungumeta Rynt kuwa tazo cikin sakin fuska saliha tace "amarsu ta ango ya amarci?murmushi kawai Rnyt tayi snn tace"nidai yasu umma? Lafiyar su qalau tana ma gaida ke ,ta fad'i hkne tare da ajiye basket d'inda ke hannunta tace"ga break fast inji umma,Rynt tace"mun gode" Byn sun zauna saliha ke cewa yaya fa?Rynt tayi kmr ma bata ji ta ba tace"wai shin saliha yaushe ne kika ce zaku koma makaranta? Saliha tace "kinsan na gaya miki cikin satin nn hutun mu ya qare sae aurenku yazo ya tsaida mu amma yanzu rnr lahadin nn zamu koma,Rynt tayi shiru can tace"to yaushe ne ake saka sabbin d'auka? Da zarar mun tafi yanzu munyi third term muka dawo gida mukayi hutu se mu koma first term to a lokacin ne ake kai sabbin d'auka sbd anyi canjin aji,yanzu za'ayi kmr wata nawa kafin haka don ni tunda inna tamin albishir d'in bokon nn na qagu naga na fara boko nn wlh,saliha tace"hm boko ko wahala ,komai wahalar sa zan so nayi saliha sbd a rayuwa ba abinda ke birge ni kmr ilimi, gskyr ki ne Rynt sbd ba abinda ya kai ilimi dad'i.....qofa suka ga an tura koda suka duba Ameera ce yamutse da fuska tace da saliha"wae ke a nn kika shigo, nikam ki sameni 6angaren anti malika, saliha tace"to sae idan zamu koma xaki ganni" nn Ameera ta ka6a kai ta fita,Rynt tace"ai da kin bita kun tafi d'in"saliha ta ta6e baki tace"um um sae idan zamu koma" Rynt bata sake cewa komai ba sae zama sukayi zasu ci abinci sae ga wani saqon abinci daga gurin inna, sosai Rynt taji dad'i sbd abincin da take mugun so ne inna ta aiko mata. Ameera kuwa koda taje 6angaren su malika ko bud'e qofa basuyi ba sae da tayi ta fmn danna door bell snn sae can ta samu aka bud'e . Man ne da malika rungume a jikinshi da gani yanzu ne tashin su don malika farin bedsheets ma ne a jikinta man kuwa yana sanye da white bathrobe yayinda fuskar sa take d'aure tamau yana kallon Ameera yace"lfy zaki mana wnn sammako hk?kafin Ameera tace"komai malika tace"haba my man ba qanwar ka bace? Ko qanwa tace sae tazo ta takura ni, kiss ta d'ora masa a gefen fuska tace"kuma fa tayi laifi amma ayi haquri ta shigo ta zauna sae muje muyi wanka ko,lumshe mata ido yayi alamar suje d'in ,ba tare da kowanen su yace da Ameera ta shiga ta zauna ba suka juya zasu tafi, malika ta kalli mohd tace"my man me xai hana ta d'aura mana break fast kafin mu fito don wlh yunwa nake ji"ba musu ya juyo ya kalli Ameera da bata riga ta shigo ba yace"ke shigo kije kitchen ki d'aura mana girki" Ameera ta shigo tare da rufe qofa tana ji kmr ta fasa ihu don ta tsani aiki ba kad'an ba. Mohd kuwa suna shiga d'aki malika ta jefar da bedsheets din jikinta ta dawo nakedness,hm mohd sae d'aukar ta yayi suka je toilet. Bayan sati 1 da faruwar haka tuni su saliha sun koma school ,mohd da malika kuwa sae cin amarcin suke inda ko sau d'aya mohd bai ta6a leqa 6angaren Rynt ba. Sam Rynt bata damu ba wacce har yanzu inna na aiko mata abinci,kuma bata da wani kad'ai ci sbd still mami na nn da kullum tare suke cin abincin su suna kallo. Yau tun da safe da suka tashi mami keta kuka ita gida take son zuwa gun ummarta duk Rynt ta shiga damuwa tayi rarrashi har ta gaji amma fafau taqi shiru ita sae taje taga mamarta. Ba yanda Rynt ta iya dole ta shirya dmn kaita gida tunda ba waya ne da ita ba bare ta kira azo a d'auke ta kuma ko banza tana son zuwa gida don zaman banzan nn ya isheta tana son komawa islamiyya. Hijabinta har qasa ta zuba ta jawo hannun mami suka fito suna kawowa harabar gidan ta sami kanta da mamakin ganin mohd zaune kan resting chair shida wani mai kama dashi sak har ma baka babance su,sam mami bata kula dasu ba sae kuka ta ajiye wae Rynt ta d'auketa ita bacci take ji,nn Rynt ta d'auke ta tare da d'aura ta kan kafad'a sae jin tayi tace "lah anti ga yaya da anti amarya sun fito"a hnkali Rynt ta juya bayanta don ganin wad'anda mami ke nufi sae kawai taga mohd shida malika ta kalli gun resting chair taga still wad'an can su biyun suna nn zaune abinsu suna fira ga kuma mohd shida malika tsaye mutum uku kenan fa iri d'aya nn kan Rynt ya d'aure sosai tana tunanin shin dama su en uku ne. Kuyi hqr da wnn. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:19PM, 1/25/2017] Ummi Ya: [ 1/11/2017] 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 🔮🔮🔮 _*page*_ *```25```* Ita tasan a qauyen su akwai en uku amma biyu ke kama da juna se d'ayar ta fita daban amma su wad'anan su duka uku kama suke har ba'a banbance su........Malika ce ta katse ta da tunanin da take da tace"my man me wnn abar ta shigo yi mana a gida! fita batun malika yayi yace da Rynt "ina zaki tafi?tace"gida mana"wa kika tambaya?ta6e baki tayi tace"tambaya"sae kawai ta juyawar ta zata wuce mami ta qwace daga jikinta ta tafi da gudu gun wad'an can mutane dake fira,man kuwa ya dakawa Rynt tsawa yace "kar ki kuskura ki qara ko tako d'aya!Rynt ta juyo shaye da toka tare da watsa masa idanuwanta a cikin nashi kafin yace komai Malika ta riga shi da cewa "wae bala'i ni ban gane ba!ko kana nufin ka aureta d'in!yace"wace magana ce kuma wnn koma daga ciki ki jirani,tace"kam bala'i har akwai wata mace da ta isa!hm!ai kuwa yanzun nn zaki bar duniyar nn baki shirya ba!nn ta duqa cikin zafin nama ta ciro takalminta mai d'an karan tsini tayi kan Rynt zata doka mata a ka,mohd ya riqe takalmin ya kuma riqe malika dake fizge fizge zata qwace kanta,yace"meye haka ne malika aurenta dake kaina dashi da babu fa duk d'aya don ba kulata zanyi ba kinsani, cikin masifa tace"wlh koma yaya ne bazata rayu a matsayin mtr ka ba don sae na rabata da duniyar nn idan har baka sake ta ba,,a natse yace be wise mana malika na gaya miki fa aurena da ita na d'an wani lokaci ne kuma kinsan halina duk abinda nace hk ne koda sama da qasa zasu had'e kuwa, ya fad'i hakane tare da rungume ta a qirjinsa,ita ko ta fashe masa da kukan shagwa6a tace"to kasan yanda zakayi da ita don wlh bana son na qara ganinta a gidan nn!to naji daina kukan ,nn yajata yana rarrashi ya shigar da ita cikin gida ya dawo. Ya samu Rynt bata nn da ita har mami, kenan ta fita yayi shu'umin murmushi snn ya qarasa gurin en uwanshi, yace"ina wnn yrnyr take? D'ayan yace " ta fita yanzu but me yake faruwa ne kaida matn naka? Yace"is nothing ku tashi muje kuyi sallama da malika d'in sbd fita zamuyi yanzu zuwa gaida su Abba,nn suka tashi suka shiga daga cikin gidan. Rynt kuwa da qyar ta sami napep sbd yanayin anguwar , basu zarce koina ba sae gidan su man suna shiga suka had'u da Abba zai fita, Rynt ta durqusa da ladabi tana gaida shi, fuskar shi wasae yake amsa mata gaisuwar snn ya dafa kan mami yace"autar mama ya sabuwar anguwar taku? ba dad'i kullum mu kad'ai a cikin gida daga ni sae anti ba mai kawo mana fira kuma mu kad'ai ke baccin mu yaya baya zuwa taya mu,kai Abba gabad'aya ma tunda mukaje gidan sae yau kad'ai da zamu fita naga yaya sun fito shida anti amarya zasu tafi anguwa har mai wae Anti amarya ta tashi du......Rynt ce tayi saurin kwa6ar ta Abba kuwa ya shiga jinjina kai yace"lallai yau zai zo ya same ni a gidan nn" ya sake cewa "shiga daga ciki Rynh zai zo ya sameni ne yau" 6angaren su saliha suka tafi wanda kafin su shiga sae da Rynt ta kwa6i mami kan kar ta sake irin srtn nn. Murna sosai umman saliha tayi da ganin su, sae dai Rnyt bata wani jima sosai ba tace"zata je ta kaida hjyr su pretty da kuma sauran mutanen gidan snn se ta tafi gidan inna. Haka ko akayi ta tafi kowane 6angare ta kaida su sae dai 6angaren hjyr pretty ba irin sallamar da bata yi ba aka qi amsa mata bayan kuwa pretty da hjy suna jinta sukayi banza da ita, tayi zama har ta gaji da qarshe tayi tafiyarta. Mohd kuwa suna shigowa gidan shida malika ya had'u da fushin Abba don yayi masa fad'a sosai ,mohd ya cika fam dan duk d'aukar sa Rynt ce ta kawo qarar shi,don har quduri ya d'auka a ransa sae yayi maganin ta idan suka koma gida,don ba abinda ya qara 6ata masa rai irin yanda Abba ya tilasta shi kan cewa duk safiya dole sae yaje duba lfyr Rynt ko ba ita keda duty ba kuwa. Rynt kuwa tana zuwa gidan inna ta had'u da motar man a nn harabar gidan bata damu ba ta shiga abinta cikin gidan ta same su su biyu suna ta fira da inñà ta gaishe su shaye da toka dan ta d'auka ko man na cikin su ,snn ta gaida inna cikin sakin fuska yayinda ta washe haqora tana fad'in marhabin lale da Rynh nn ta shiga tmbyr lfyr gidan su Rynt tace"duk lfy qalau inna tace" ina er tafiyar ki mami? Tana can gun mama wae sae gobe ko zata dawo guna,ayyo to inace lafiya qalau kuke zaune da abokiyar zaman taki ko?lfy qalau inna ina baaba hurera ?ai baaba hurera taje qauye bikin wata jikarta ta barni ni kad'ai cikin kewa, Rynt tace" Allah sarki yaushe zata dawo?inna ta d'aga kai sama tana tunani can tace"yauwa inaga gobe ne don rnr litanin tace min zata dawo,Rynt tayi shiru tana ji kmr tayi zamanta har sae gobe ta koma dai dai an maida mata mami don dai baccin nn ita kad'ai take yiwa tunani.....tunaninta ya katse da jin wad'anda ta samu sunà sallàma da innà yayinda inna keta zuba musu albarka tana godiya kan irin damen kud'in da suka ajiye mata ta bisu da rakiya tana fad'in"har zaku tafi to Allah kiyaye hanya sae kuma kun sake zagayo mu duk da dai ba nan kusa ba kam tunda ba zowa kuke ba sae da lalura ,d'ayan yace"to inna kinsan yanayin aikin mu ne sae a hnkli daga haka Rynt ta daina jiyo zancen su sbd sun mata nisa. Bayan inna ta dawo ta d'auki kud'in da suka ajiye mata washe da baki tace"kin gansu en albarka abokan haifuwar muhammadu ne dake zama qasashen turai tare da matansu. Rynt tace"en uku ne kenan inna? Eh ai en uku ne,tace am inna ya naga motar maigidanki amma kuma baya cikin su?yo ai wad'an nn da kika gani maida abin wani naka ne haka suka taso tun suna yara bakya banbance wnn abin wnn ne a tsakanin su sae dai idan kinsan ainihin mai shi don yanzu kinga sun taho cikin motar muhammadu shi kuma yana can cikin motar d'ayan su. Rynt tayi shiru yanzu kenan ya zatayi ta fhmci waye ya kashe mata mahaifi a cikin su ukku nn can ta d'ago a hnkli tace"inna hln yaushe ne rabon su da zowa nn qasar naji kince suna jimawa kafin suzo,inna tace "sosai kam suna jimawa don zasuyi shekara kafin su sake zowa amma a cikin wnn shekara kusan zuwan su uku kenan sbd bukukuwan da akayi tayi a dangi sbd ko nasiru da Fatima a cikin shekarar nn akayi bikin su kuma sunzo snn da za'ayi bikin zainaba ma sunxo wato wacce ke biwa nasiru inace kina jinta a bakin saliha,kuma ai kinga ma tazo bikin nn naku wacce tun daga bauci mijinta ya kawota akayi biki tare dashi snn suka koma. Nn inna ta kawo qarshen zancen, Rynt kuwa gabad'aya taji lissafinta ya kunce yayinda take ji a ranta bafa zata iya barin ko waye ba har sae ta d'au fansa amma kuma a cikin su ukkun nn taya zata san waye yaje qauyen su har ya kashe mata baffanta ko kisa na wulaqanci da rashin tausayi ,haqiqa ta yarda da qaddara amma baxata d'auki kisan mahaifinta a qaddara ba sbd ya shigo da gayya a cikin shi dmn da ba don reverse d'inda yayi kan mahaifinta ba da inshaAllah mahaifinta zai rayu shine abinda ke qara qona mata rai idan ta tuno da hkn......a cikin tunanin tane wani 6angaren zuciyarta ke bata shawara ta yanda xata sami mafitar gano waye a cikin su shine ta jure ta kasance mai kusanci da mohd sannu sannu har shima ya d'an fara sake mata da haka da haka zata gano waye a cikin su ta hnyr masa wata tambaya......inna ta katse ta da cewa "lfy Rnyh tun d'axu kinyi shiru kmr mai wani tunani,a kafaice Rynt ta share en hawayenda suka zubo mata tace"ba komai inna kawai dama ina son muyi zancen komawa ta islamiyya ne ,inna tace"to Rynh ai mijin naki ya kamata ki tuntu6a sae ya samar miki wata makarantar ta matan aure,Rynt tace"to inna" 9:00pm Tuni Rynt ta koma gida ita kad'ai a d'aki duk kewar mami ta cika ta don yrnyr akwai surutu sosai wacce da ace tana nn da yanxu duk ta cika ta da srt shiyasa tayi kewarta ba kad'an ba. Tayi minti 30 tana tunanin yanda zata shiga bayi tayi wanka kan baqin tsoro sae can tayi addu'ar ta ta shiga,haka tayi wankanta ba tare da ta wanke fuska ba don ganin take in ta rufe ido koda zata bud'e zata ga wani abin tsoro, wacce duk qarin jin tsoron nn bai wuce sanin ita kad'ai ce a d'aki ba don lokacinda mami na nn lafiya lau take yin wankanta ba wani shamaki. Tana fitowa idonta ya hango mata abu tsaye a qofar d'akin a razane ta buga ihu ta kwasa aguje zata koma bayi, mohd da dama shine tsaye yayi hanzarin jawota da qarfi har sae da ta fad'o kan qirjinsa ta koma sakin wani ihun sbd zanin ta da ya rabu da jikinta ,sae duk ta rud'e tana wani kakkama jikinta bayan cewa sanye take da qaton hijab har wuce guiwa,wani kallon banza mohd ke mata snn ya kalli zanin ta da ya sa6ule ya sake d'ago idonsa yana kallon fuskarta ya kamo wuyan hijabinta yace"idan na raba ki da wnn hijabin sae ki gaya min dalilin fitar ki gidan nn da kuma qarata da kika kai a gurin Abba,sosai ta fiddo manyan idanuwnta masu cike da jin tsoro tace"Aa dan Allah kayi haquri wlh shi kad'ai ne a jikina! Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:19PM, 1/25/2017] Ummi Ya: [1/12/2017] 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 🔮🔮🔮 _*page*_ *```26```* Kauda kansa yayi gefe dan shi sam tunanin hkn bai fad'o masa ba shidai kawai dukan ta yaso yi har sae jikinta ya gaya mata. Ya kalle ta ta6e da baki yace"badai akwai fata a jikin ki ba wacce zata aika miki da saqona har ixuwa daqiqiyar qwaqwalwarki" Rynt ta wani qara bud'e manyan idanuwanta ganin yana zare belt d'in wandonsa , ta fizgi jikinta da qarfi tace"wae dukana zakayi, don Allah kayi baquri wlh duka fa da zafi" Yace"da zafi?eh wlh don Allah kayi haquri bazan sake fita ba sae da izinin ka na rantse!bai kula ta ba yayi cikinta ya fara dukanta kan qafafunta gunda hijab bai qarasa kai ba , ihu take sosai tana bashi haquri amma fafau yaqi haqura sae da ya zane mata qafafu tas snn ya dakata tare da nuna ta da yatsa yace"idan har tunanin kike kinzo nn gidan don jin dad'i shine har kike fita anguwanni to ki cire kisa a ranki nn tmkr kurkuku kika shigo don haka daga yau ko qafar ki kar na qara ganin ta fito daga d'akin,nn ya kama kunnen sa yace"kinji me na gaya miki? da sauri ta gyad'a masa kai cikin kuka,nn wyr sa tayi qara ya d'aga had'e da fita d'akin Rynt kuwa ta had'e kanta da guiwa tana ci gaba da kuka ,takai hannunta cikin hijab tana shafa qafafuwanta da duk sukayi shatar belt. Tana jin za'a shigo d'akin tayi saurin d'aukar zanin ta ta d'aura ,mohd ne riqe da hannun mami ta tafi da gudu ta rungume Rynh wacce tayi saurin share hawayenta kar mami ta gani , mami tace"Anti na dawo ne sbd inajin dad'in zama gurinki sbd kullum kina koya min karatun islamiyya ko yau zaki koya min kafin muyi bacci ko? Dan guntun murmushi Rynt ta qirqiro ta gyad'a mata kai kawai don har lokacin man na tsaye yana kallon su, mami ta maida dubanta gare shi tace"yauwa yaya d'azun da mukaje gida nida anti har nake gaya ma Abba cewa kullum kullum mu kad'ai ne a cikin gida ba mai kawo mana fira daga ni sae anti har kai bama gani sae yau kad'ai muka ganka kaida anti amarya zaku tafi anguwa sae naji Abba yace wae zaka zo ka same shi ne ai,to yaya kaje ka same shi d'in don wata qil aiken ka zai yi ko?kallon su yayi da ita har Rnyh d'in kafin yace komai mami tace"yaya wai anti d'azun da mukaje gida har na gaya ma Abba haka tace min wae kar na qara gayawa kowa haka kuma wae na rage yawan srt ba kyau wae hakane yaya?hakane mami,yayi mgnr ne a takaice ya kuma juya zai bar d'akin , mami taje da gudu ta riqo hannun shi tare da d'aga kanta tana kallon shi tace"yaya yau ma baza ka taya mu fira ba tafiyar ka zakayi?eh zan tafi ne naci abinci,nima yaya zan bika muci abinci,yace"to muje"Rynh na kallo suka fita taje ta kwanta ruf da ciki tana ci gaba da kukanta . Sae goma da rabi mohd ya dawo d'auke da mami wacce tayi bacci ya samu ita ma Rynt tayi bacci sae dai kallo d'aya xakayi mata kasan da tsoro baccin ya d'auketa don duk ta cusa fuskarta cikin pillow ta kuma damke pillow kmr wacce za'a qwacewa shi , yaje a hnkli ya kwantar da mami snn ya kalli Rynt wacce cikin qaton hijabinta tayi baccinta nn idonsa ya fad'a kan santala santalan qafafuwanta da hijab bai ida rufewa ba da har yanzun suna d'auke da shatar dukan da ya mata,ya kauda idonsa snn ya fita yaja musu qofa ya rufe. Washe gari Rynt ta tashi cike da jin yunwa sbd jiya da dare bata ci abinci ba tayi bacci. Tana gama yi ma mami wanka ta shiryata,mami tace zata je gun yayanta nn mami ta fita ita kuma Rynt taje kan bed ta zauna cike da tunanin inda zata sami abinci tunda yanzu kam inna bazata qara aiko mata ba. Tana nn zaune yunwa ta cita har ta gode Allah sae duk rayuwarta ta baya ta dawo mata nn ta had'e kai da guiwa ta fara kukan tuna baffanta, sae jin tayi an turo qofa ta d'ago fuskarta a hnkli don ganin wanda ya shigo. Mohd ne yaja ya tsaya a nn bakin qofar ya jingina tare da sanya hannuwansa a aljihun wadonsa yana kallonta ita ma tana kallon shi da idanuwanta da suke cike tap da qwallah ta taso cikin tafiya kmr bata so har ta qaraso gurin shi tayi tsaye tare da sadda kanta qasa tana kallon farin tiles d'in d'akin,mohd ya fiddo d'ayan hannunsa a aljihu ya d'ago fuskarta dashi yayinda hawayen idonta ke silalowa a hnkli kan kumatunta sae dai still idonta na qasa sae da yace"mene ne"snn ta kalle shi tare da fad'in yunwa nakeji tun jiya banci komai ba" To shine zaki wani ajiyewa ma mutane kuka !ni ba yunwa nake ma kuka ba ai,to me kike ma kuka? tace"nidai ka taimaka min da abinda zanci.... idan anqi fa, Allah zai taimake ni,au kinsan da Allah kuma kika ce ni na taimaka miki,shiru ta mishi ta komawarta kan gado tayi kwancinta ya saki guntun tsaki ya fita daga d'akin. Ba jimawa sae ga kukun gidan ya kawo mata abinci tayi mamaki don ita kanta roqonsa kawai tayi bata d'auka zatayi nasara ba , don a nn kwancen da take har ta fara tunanin tashi ta sami ruwa tasha kmr yanda ta saba yi a qauye. Sama Sama taci abincin sbd abincin duk rabinsa ganye ne ita kuwa ba son ganyen take ba tunda ba'a saba ba, don ko yanzu ture ganye tayi gefe taci abinda take iya ci tabar saura, bayan d'ayan plate d'inda ta ajiyewa mami. Bayan kwana d'aya da faruwar haka Rynt na zaune a tsakiyar gado ta lanqwashe qafafu tana karatun qur'ani cikin muryar ta mai dad'in sauraro ga duk wanda yaji,mohd ya shigo d'akin yayi tsaye tsawon lokaci bata sani ba sae karatu take abinta, sae da yayi gyaran murya snn tasan da shigowar shi ,kallon sa take ba yabo ba fallasa haka shima sae dai kuma zama d'aya ya sha mata toka ya juya tare da fad'in "biyoni muje ki gyara min d'akina" Ba musu ta ajiye qur'aninta ta bishi. Tsarin gidan tsari ne da d'akunan matan shi suka saka shi tsaka wanda dole duk wacce zata je d'akin shi sae tazo ta main falo take zuwa kuma in an shiga qofar da zata sada ka da 6angaren shi sae an hau upstairs kafin ka kai ga d'akinshi. Rynt sae rarraba ido take tana kallon koina don dai gurin ya zamar mata kmr aljannar duniya,suna shiga d'akin mohd ya juyo gareta yace"kinga d'akin sae kiyi ki gyara min kan lokaci" Gyad'a masa kai kawai tayi,shi kuma ya fita yaje 6angaren malika,ya sami malika jikin wardrobe yaje ya rungumo ta ta baya tare da fad'in"malika had'a min kayana dake d'akin nn zan koma d'akina ne yau"ta juyo tare da qara rungume shi snn tace"gsky ba inda zaka je muyi zaman mu guri d'aya yafi don ni bazan iya whlr jeka ka dawo ba" yace"hqr dai zakiyi malika sbd komawata d'akina shine saiti "ta d'ago a fusace tace"ok kana nufin zaka raba mana duty tsakani na da wnn abar! girgixa kansa yayi yace"ko d'aya kuma kwata kwata ki cire wnn tunani a ranki kawai dai ina buqatar komawa ne"to gsky ni bana buqatar ka koma can! yace"A'a fah!cikin masifa tace"to wlh duk ka koma sae na bika!ya gyad'a kafad'a tare da fad'in "no vex yanzu sae ki had'a mana kayan ko? murmushi tayi snn tace"yanzun naji bayani don wlh ban yarda da zamanka kai kad'ai ba"yace"to da sharad'i ba gabad'aya fa xaki tare guna ba...kmr ya?kawai bacci zaki riqa kai min sbd bana son kowa na shigar min 6angare,sbd frnds d'inki sun fiye zowa kin sani ba kuwa zai yiyu kina zuwar min dasu 6angarena ba,ta wani 6ata fuska tana kallon shi tace"to meye a ciki don naje dasu kawai kai dai na fhmce ka so kake da rana ka riqa zuwa kana holewa da wnn yrnyr,cikin daka mata tsawa yace"wlh kar na koma jin kin ambata min wnn yrnyr idan muna zancen mu!bcs i am absolutely hate her!don haka yawan yimin zancenta kan iya sa qiyayyar da nake mata ta dawo gare ki be careful!daga haka ya juya zai fita daga d'akin , malika tayi saurin rungumoshi ta baya, tare da fad'in "my man yi hqr zan kiyaye kaji"sae da ya sauke ajiyar zuciya snn ya juyo tare da riqo kumatunta yace"malika ina mata d'aukar baiwa ne ba mata ba amma ke kinxo kina alaqantani da ita a matsayin matata wlh malika da kinsan baqin cikin da nake ji da hkn da ko da kuskure baza ki ambata min ita ba,kayi hqr my man bazan sake ba,fuskarta ya shafo tare da fad'in "shi kenan ya wuce muje mu had'a kayan ko?murmushi ta sakar mai taja hannun shi suka nufi wardrobe. Rynt kuwa nn take ta gyara d'akin tsaf don dama ba wani datti ne dashi ba ,zata fita kenan idonta ya hango mata wani photo na mohd su uku wato shida abokan haifuwar shi, ta d'auko d'an frame d'in tana kallo nn ta fhmci akwai rubutun da akayi kmr fulawa dan sae ka kula da kyau kake fhmtar rubutu ne akayi , Aamil,Amir &Aminullah shine a rubuce ta qasan kowanensu. Shafa rubutun ta shigayi sbd ba qaramin kyau ya mata ba yayinda ta shiga kallon fuskokin su cike da son gano meye banbancin su,sae ga mohd rungume da malika sun shigo d'akin,malika na ganin abinda Rynt keyi tayi saurin d'agowa daga jikin man tace"kaga er iska photonka fa take kallo shine har da wani shafawa! taje fuuu!ta fizgi photon tare da kife Rynt da mari tace"keda aka sa gyaran d'aki me kuma ya kaiki ga photon mijina er iska ,tambadaddiya dake nake! ki gaya min ko wlh na qara miki wani marin ynx!nn mohd yazo gun Rynt wacce ta dafe kuncenta yace cikin kakkausar murya"dan ubanki aikin da na saki kenan ko kuma ni sa'anki ne da zaki d'auko photon mu kina kallo!bari kiji wlh daga yau duk nasaki aiki naga sa6anin haka ubanki na lafira ma sae yafi ki jin dad'i!da sauri Rnyt ta d'ago idanuwanta da sukayi jajir suka ciko da qwallah tana kallon shi. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:19PM, 1/25/2017] Ummi Ya: [1/13/2017] 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 🔮🔮🔮 _*page*_ *```27```* Tsawa mohd ya daka mata mai firgitarwa tare da fad'in"get out!da sauri Rynt ta tafi har tana had'awa da gudu taje d'aki ta fad'a ruf da ciki kan bed tare da fashewa da wani irin kuka mai ban tausayi. _Ta yaya zan barshi! bayan shine silar rabani da farin cikina kuma shine silar zuwana birni har na had'u da qaddararren aurenda nake ganin wlqnci haka, lallai idan mohd ya kasance shine wanda ya kashe min mahaifi a cikin su ukun nn fansar da zan d'auka akanshi mai munin gske ce._ _Allah sarki yaya anwar nsn da kana raye haka ta faru dani da ka bimin haqqina ba tare da na aiwatar da abinda bai dace dani ba._ Tana magana ne a cikin zuciyarta yayinda take ci gaba da kuka mai cin rai. Tana cikin hakane mami ta shigo d'akin, Rynt tayi saurin share hawayenta wasu suka sake zubowa dai dai mami ta hau gadon d'auke da ledodi a hannunta ta kalli Rynt tace"anti wa ya dake ki kike yin kuka?share hawayen tayi tace"ba wanda ya dake ni"amma kuma kikeyin kuka ko wani ne ba lfy don naga yau da mukaje asibiti nida yaya Nasir duba wani yaya munir abokin yaya man ummansa sae kuka take tayi sbd ko magana baya yi ance ma sae an fita waje dashi ko zai sami lafiya,wasu hawaye ne suka sake zubowa Rynt tace"yaya munir yayan su safiyya? Eh anti shi ashe kin sanshi,kuka ta shiga yi mara sauti ,mami tace"anti umma fa tace min ba kuka ake yiwa mara lafiya ba addu'a, kinji anti ki daina kuka ki masa addu'a, had'e kai da guiwa Rynt tayi tana ci gaba da kuka ,mami ta dafa ta tana fad'in"anti addu'a fa zaki masa ba kuka ba,nima da nake er qararrama ban masa kuka ba sae cewa nayi Allah ya bashi lfy,naji mami zan masa addu'a nima, ta fad'i hkne yayinda ta d'ago tana share hawayenta, mami ta jawo ledodin da ta shigo dasu guda biyu tace"Anti yaya nasir ne ya saya mana chocolate nida ke ga ledar ki kar6i,Rynt ta kar6i d'ayar leda ta d'aura kan bedside drawer,mami kuwa sae kallon idanun Rynt take da sukayi jajir tace"Anti hln yaji ya shiga miki ido da na samu kina kuka"girgiza kanta kawai tayi,snn tace"tashi muyi sllr zhr sae mu yiwa yaya munir addu'a ko?to anti daga nn ma mu roqi Allah yasa mu anjannah muci kayan dad'i ko?Rynt tayi d'an murmushi snn taja hannun mami suka nufi bathroom tare sbd haka suke kullum in zasuyi arwala tare suke shiga dmn arwala Rynt ke koyawa mami amma wani lokacin sae ta fara shiga in ta kama ruwa snn ta kira mami ta shigo. Bayan sun gama sallah mami ta d'auko ledar chocolate d'inta tace"Anti zanje na kaiwa anti amarya chocolate taci" Rynt tace"to sae kin dawo" ba jimawa sae gata ta dawo tana cin chocolate tace"Anti qofar anti Amarya a rufe take inaga ta fita,na bari gobe na sake kaimata ko? "eh"shine kad'ai abinda Rynt tace don sae tunanin rashin lfyr munir take. Washe gari da safe ko break fast basuyi ba mami ta jawo ledar chocolate ta fita wae zata kaiwa anti amarya ta d'iba. Fitar ta keda wuya ta jiyo kukan mami ta fito da sauri har tana had'awa da gudu tana isowa main falo ta had'u da mohd shima ya fito sbd jin kukan mami da yayi ,mami taje da gudu jikin Rynt inda cikin kuka sosai take nuna malika ,mohd yace da malika me kika mata ne! shaye da toka tace"sanin kanka ne qanwar nn taka baqin srt tsiya ne da ita ,tazo ta sameni ina bacci daga kawo min ledar chocolate tayi wae na d'iba nace mata bana so bai isheta ba sae da ta wani cika ni da srt shine ni kuma na mareta, jiki sanyaye ya kalli mami wacce bakinta ke fitar da jini ya jawo hannunta yasa tissue ya goge mata jinin yace"ki daina takura anti amarya idan tana bacci kinji, cikin muryar kuka tace"Allah yaya qarya take ba bacci take ba "malika ta dallah mata harara tace"dan ubanki ni ke qarya "a fusace ya d'ago yace"malika mind ur tongue qanwata ce fa kike zagin ubanta"to kai baka ji me tace min bane!kuma indai zagin ubana ne ai akanka na koya ,tsaki yayi ya kalli Rynt wacce yake ganin kmr duk laifin ta ne yace"da Allah malama jata ku tafi! Rynt ta kalle shi snn ta d'auki mami tana share mata hawaye tace"yi hqr Allah zai isar miki" Malika tace"jar uba! ke ni kike gaya ma magana! ta tafi fuuu!zata kaiwa Rynt duka ,mohd ya jawota yace"barta kawai zanyi maganin ta ne,nn ya tafi da ita sae masifa take tana sirfàwa Rynt zagi har suka shige 6angaren mohd. ta6e baki Rynt tayi snn ta wuce d'auke da mami. Da dare mohd ya shigo d'akin Rynt ya sami Rynt da mami suna pillow fight sae dariya suke suna dukan pillown juna har Rynt tayi nasarar da pillown mami ya qwace ya fad'i qasa nn Rynt ta tashi cikin dariya tana mata gwalo tana fad'in "ko yanzu na cinye ki"cikin shagw6a mami ta turo baki,sae kuma ta washe baki ta tashi da sauri ta bud'e wardrobe ta d'auko qatuwar teddyn ta da tasan Rynt na mugun jin tsoro tayo kan Rynh aguje zata liqa mata,Rynt da ko ganin ta bata son yi ta rufe ido ta kuma kwasa da gudu zata bar d'akin,sae jin tayi ta fad'a jikin mutum nn ta fasa wani irin ihu ta zube gabad'aya a jikin man. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:19PM, 1/25/2017] Ummi Ya: [ 1/16/2017] 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 🔮🔮🔮 _*page*_ *```28&29```* Tsaki mohd yaja tare da ture ta daga jikin shi, kan ta kai qasa yayi saurin tarbota dan sae a lokacin ya fhmci suma tayi,ya kwantar da ita nan qasan tiles ,mami kuwa ta jefar da teddy tazo da gudu gun Rynt ta saki ido tana kallon Rynt dake kwance, mohd yace"je 6oye teddy ki d'ebo min ruwa" Mami taje ta maida teddy snn ta kawo masa ruwa ya kar6i ruwan ya shiga yayyafa ma Rynt a fuska,firgigit ta tashi tana ihu tana fad'in"mami ki daina liqa min wnn abun bana so dan Allah"ta qarashe mgnr kmr qaramar yarinyar da zatayi kuka,wacce sae a lokacin ta kula da mohd da ko lokacinda taci karo dashi ta d'auka ko teddy ce,shiyasa ta qara firgicewa har ta kaita ga suma . Mami tazo gab da ita tana kallon Rynt wacce tayi zaune ta had'e kai da guiwa yayinda jikinta ke ta rawar tsoro ta dafa ta snn tace"anti kiyi haquri kinji bazan sake ba"kafin Rynt tace komai mohd yace da mami,"d'auko min teddyn naje dashi d'akina idan kin buqata sae kije d'akina kiyi wasa a can ko? Mami ta gyad'a kanta tare da tashi ta d'auko mai teddyn ta bashi ya kar6a tare da duqawa zai d'auki agogon sa da ya fad'i kusa da Rynt,dai dai Rynt ta d'ago fuskarta da idanunta ke cike tap da qwallah,ganin teddy a hannun shi yasa tayi saurin matsawa tare da tura masa agogon sa da ta fhmci zai d'auka, sae da ya kalleta snn ya d'auki agogon ya fita. Mami tazo jiki sanyaye gun Rynt tace"Anti kin haqura ko?Rynt ta gyad'a mata kai tare da share hawayenda suka zubo mata,snn tayi d'an murmushi tace"ba komai ya wuce" Daga haka ta tashi sukayi shirin bacci suka kwanta. Mohd kuwa 6angarensa ya nufa yana shiga ya jefar da teddy kan sofa snn yaje ya kwanta kan bed tare da ciro wyrsa a aljihu ya fara latse latse. Malika ce ta shigo d'akin cikin rgrta ta bacci dani da babu taje kusa dashi ta kwanta tana kallon abinda yake yi a waya, ta kalli fuskar shi snn tace"my man ashe kana game"yace"in tamin dad'i ba"ta mirgino kan jikin sa tare da kai hannu tana shafa sajen fuskar shi tace"my man nifa ban gane ba har mun shigo cikin sati na biyu da aure amma banji kana zancen zamuje honeymoon ba" yace "malika nida ke son komawa bakin aiki ina kuma zancen wani honeymoon" ta 6ata fuska tana kallon shi tace"ba wani nn gsky ni sae munje honeymoon tunda ba fina akayi ba"to shikenan zamu je d'in" kiss ta bashi tare da fad'in "tank u"yayi murmushi yaci gaba da aikin sa kawai,nn malika ta shiga qoqarin hana mishi game d'in don sae wasu abubuwa take mishi a jiki har ta kai ga ta qwace wyr tana qoqarin had'e bakin su, ya kauda bakinsa gefe snn ya koma kallonta sbd buttons d'in rgr sa da ta shiga 6allewa ya riqo hannunta yace"malika wae ke ba kya gajiya ne,naga yaushe yaushe ne muka rabu" to my man kai d'in na daban ne kasani shiyasa bana gajiyawa da kai"ta qarashe mgnr tare da kashe mai ido d'aya ,yace"to muyi bacci har gobe don yanzu kam ngji"ta wani 6ata fuska tace"gsky nifa ina buqata" ya salam shine abinda ya fad'a a ransa har ga Allah baya son yawan laluboshi da take wace irin mace ce da tun auransu bata ta6a bashi rana d'aya ya huta ba har yau,nn yace"ok ina zuwa"ya tashi ya fita sae gashi ya dawo d'auke da fresh milk da cups ya kalleta d'auke da murmushi yace"bari musha tukun ko" bai jira amsarta ba ya tsiyaya mata fresh milk ya bata, har ta shanye cup d'in tas shi bai ko fara shan wacce ya zuba ma kanshi ba,ya kar6i nata cup yace"na qara miki ne? Ta girgiza kanta tare da matsowa kusa dashi ta kwantar da kanta a qirjin sa, daga nn tayi bacci don dama maganin bacci ya zuba mata don kawai ya huta da jarabarta. Bayan kwana uku da faruwar hakane zuwa honeymoon d'insu ya tashi dan har ma ga gobe zasu tafi shiyasa tun safe yakai malika gidan iyayenta don ta musu ban kwana, Rynt kam bata san abinda ake ciki ba kawai dai kullum da safe mohd na shigowa 6angarenta yaja mami suyi breakfast ita kuma kuku ake aikowa ya kawo mata nata,kuma in banda gaisuwa ba abinda ke had'a ta da mohd. Zaune suke ita da mami a d'aki kan bed tana koyadda mami karatun qur'ani, ya shigo ya same su , Rynt na had'a ido dashi ta kauda kai amma shi still kallonta yake sae ma cewa yayi ki taso keda mami zamu fita, daga haka ya juyawar sa ya fita mami ta bishi da gudu tana jin dad'i. Koda Rynt ta fito harabar gidan ta samu har sun shiga mota ita kad'ai suke jira,taje ta shiga motar itama. Basu zarce koina ba sae family house,mami ta tafi da gudu zuwa 6angaren su,mohd kuwa ya nufi nasu 6angare shida Rynt , suna shiga falo suka sami Abba zaune ta durqusa ta gaidashi cike da ladabi ,ya amsa mata cikin sakin fuska. Byn sun zauna da ita har mohd d'in snn Abba yace" nine nace yazo min dake kan wani rashin adalci da naji yana shirin yi da na masa magana se yace kece baki buqaci hkn ba,Rynt ta kalli Abba don ita bata gane inda zancen nasa ya dosa ba, Abba yace"batun zuwan su honeymoon ne shida malika shin kinsan da batun zuwan? Rynt da batasan meye honeymoon ba illa kawai abinda ta fhmta wani guri zasu, zuwansu da rashin zuwansu kuwa duk d'aya ne a gurinta se tace"eh" to meyasa baza ki bisu bane ko kuma shi ya hana miki? Aa Abba kawai dai ina son zan koma islamiyya ne, Abba ya kalli mohd yace"to kaji idan ita waccan d'in honeymoon ta buqaci zuwa kaji wnn islamiyya take buqatar komawa don haka sae kayi adalci a tsakanin su"yace"inshaAllah Abba, nn mohd ya tashi ya fita Rynt kuwa ta tashi zata haura sama dmn gaida hjyr su mohd Abba yace"Ai bata nn ta fita, tafi kawai abinki ku koma gida, tace"to snn ta fita" Koda ta fito mohd na jingine jikin mota yana jiran fitowar ta,bata nufi gunshi ba sae 6angaren su saliha ta nufa yace"ke ina kuma zuwa?tace " Zanje gaida mama ne daga haka bata jira amsar shi ba ta shige abinta. Bata wani jima ba ta fito ita kad'ai ba tare da mami ba don dama tun cikin mota da suna kan hnyr zowa tace in sunxo sae dare zata koma. Tafe suke kan hanya ba mai ce ma wani can Rynt tace"gidan inna fa"kallon ta kawai yayi ba tare da yace komai ba yaci gaba da tuqin sa har suka isa gida. Da dare ta fito daga wanka mohd ya shigo d'akin riqe da hannun mami ya same ta sanye da qaton hijab d'inta as usual ,ta d'auko Vaseline zata je kan bed ta shafa,ya tsaya bakin qofa mami kuwa taje da gudu gun Rynt snn ya juya ya bar d'akin yana mai jiyo yanda mami ta fara cika Rynt da srt. Washe gari tunda ya dawo daga masallaci sllr asuba ya tafi d'akin ya samu duk bacci suke da ita har mami kasancewar fashin sll Rynt keyi shiyasa bata tashi sllr asuba ba. Rynt bata da nauyin bacci ko kad'an shiyasa taji lokacin da mohd ya shigo,yana jin yanda sautin addu'ar tashi daga bacci ke fita a hnkli daga bknta snn ta tashi zaune had'e da blanket d'in jikinta wacce still tana sanye da hijabinta. Ta amsa masa sallama tare da had'e kanta da guiwa tana mishi ina kwana,ya amsa ba yabo ba fallasa sae kuma ya fita bai ce mata komai ba hkn yasa ta komawarta ta kwanta. Koda ya koma d'akin shi ,malika na kwance bata tashi ba sae sharar bacci take bayan ba irin tashin da bai mata ba kafin ya tafi masallaci, ya kalli yanda take kwance bata da maraba da tsiraici sbd gabad'aya abin rufan ta kad'an ya saura ya sauka kan jikinta,guntun tsaki yayi snn ya fara tashin ta da qyar ya samu ta motsa sbd baqin bacci ne da ita ,a maimakon ta tashi sae ma gyra kwanciya tayi,cike da takaici yace"wlh duk kika koma wani bacci za'a fasa tfyr nn ne!firgigit ta tashi tana miqa had'e da hamma tace"wayyo my man bacci bai ishe ni ba fa"komai kasa ce mata yayi don duk ta cika shi da takaici ganin ba komai a jikinta amma ko kunya babu sae wani miqa take a gabanshi, haka ta tashi ta nufi bathroom ba tare da ta yafa komai a jikinta ba. Guraren qarfe tara mohd ya koma d'akin Rynt cikin shirin sa tsaf sae qamshi yake zubawa ,ya same ta zaune da breakfast a gabanta yace"mami fa ?tace"tana bayi" yace "ok mu zamu tafi" tayi saurin kallon shi tace"to mufa zamu koma gidan inna ne, snn zancen komawata islamiyya fa ?yace"zancen islamiyyar ki babu"kmr zatayi kuka tace"amma ba haka mukayi da kai ba gurin Abba,,wani mugun kallo ya watsa mata yasa kai zai fita tayi saurin tashi ta bishi hkn yasa ya dakata tace"bafa zan iya kwana daga ni sae mami a gidan nn ba,yace "wnn kuma ya rage naki" Ya fita hk ta koma binshi ya daka mata tsawa yace"kikayi gigin na sake taka qafa ki tako taki ko wlh sae na mare ki"kuka ta fashe mai dashi tace"nidai kayi haquri dan Allah mu tafi gidan inna kuma na koma islamiyya wlh na sa raina a islamiyyan nn" A sae ki cire tunda ba gidnku bane da zakiyi abinda kika ga dama! Sautin kukanta ne ya soma fitowa ta hana faruwar hkn ta komawarta ta zauna tana jin mami zata fito bathroom tayi saurin share hawayenta yayinda mami ta fito tana fad'in " gufranaka ya Allah" ta washe baki tare da fad'in"hkne ko Anti?Rynt ta qirqiro murmushi tare da gyad'a mata kai"snn takai dubanta gun mohd da har lokacin yana tsaye bai fita ba mami taje gurin shi da gudu yaja hannunta suka fita. Tayi awa d'aya kafin taga dawowar mami. Wacce ta dawo d'auke da kayan wasa kala kala sae murna take taje kan bed tana fad'in"Anti yaya ne ya sayamin kayan wasa yace in ta wasa har su dawo wai baza su jima ba"Rynt tace"to zo kici abinci?ai anti sae da nayi breakfast kafin naje raka su yaya a airpot ,Rynt da ba tasan meye haka ba ta basar da zancen. can mami tace"lah anti na manta yaya nasir fa yana falo wae kije. Koda Rynt taje kuwa ta same shi zaune a falo cikin ladabi ta gaida shi ya amsa ba yabo ba fallasa snn yace"ko da akwai wani abunda kike buqata?ta gyad'a masa kai tare da fad'in "eh"yace"me kenan" tace"ina son na koma gidan inna da zama ne har idan sun dawo snn kuma ina son na koma islamiyya"yace"meyasa kike son komawa gidan inna? Sbd bana jin zan iya bacci daga ni sae mami a gidan, gidan nn ya mana girma sosai"indai wnn ne ai mai sauqi ne Rynh don da sannu zaki saba kuma idan wani abu kike tunanin zai faru ai akwai masu tsaro sosai a gidan kuma da yardar Allah ba abinda zai faru kinji? ta gyad'a masa kai snn yace"zancen islamiyya kuma gobe inshaAllah nn cikin anguwar zan nema miki wata islamiyya ta matan aure "tace"to nagode yaya nasir" yace"sae kuma me kike buqata? Shike nn komai bana buqata, to ga wnn ki riqa a hannun ki, tace"Aa wlh ka barsu kawai nagode inada kud'i a hannu na da inna ta ban"murmurshi kawai yayi ya ajiye kud'in kan center table ya tafi tace"masa nagode snn ta d'auki kud'in ta juya cike da jin dad'in zata koma islamiyya,yayinda nasir ya fita cike da mamakin mohd ace zai yi tafiya bai bawa mtrsa komai ba. Da dare kuwa duk ta cire wani tsoro a ranta sukayi baccin su ita da mami. Washe gari da kanta taje kitchen tayi musu break fast sbd yinin jiya duk bata ga kuku ba bai kuma kawo musu abinci ba. 8:pm nn falo suke zaune su biyu abinsu suna kallon tom and jerry. Sae ga nasir ya shigo da sallamar sa. Bayan sun gaisa ya bata leda yace" hijabin makarantar ne a ciki kuma da qarfe biyu ake zuwa a dawo qarfe hud'u . makarantar tana a nn bayan gidan ba nisa amma gobe zan zo na kaiki don kiga makarantar. Sosai tayi mai godiya snn ya tafi. Haka ko akayi washe gari nasir yazo ya kaita islamiyya mami kuwa ya kaita gida. To tun daga rnr ita ke kai kanta ta kuma maida kanta amma sae da qarfe biyar ake maida mata mami. Su mohd kuwa kusan sati uku sukayi a yawon honeymoon d'insu. Rynt kuwa sosai ta maida hnklinta zuwa islamiyya kuma rashin kuku bai kawo mata wata matsala ba don koda 1:30 keyi har ta gama musu abincin su na rana sunci ita da mami bcs kafin qarfe biyu nasir ke zowa yakai mami gida,sbd Rynt ta samu taje islamiyya kan lokaci,idan kuma ta dawo qarfe hudu sae tayi sll snn take d'aura musu girkin dare,kuma duk abinda tayi ra'ayin dafawa akwai shi a gidan matsalar ta d'aya itace kewar inna da take sosai. Rnr wata assabar ne Rynt ta dawo daga islamiyya ita da wata qawar ta suka shigo gidan kowanen su cikin niqabi,da kuma hijab d'insu har qasa da socks . A nn harabar gidan ta had'u da malika da mohd wa'anda saukar su kenan, gaban Rnynt yayi mugun fad'uwa sbd tunanin abinda zai biyo baya ita da mohd idan yaga ta koma islamiyya bada sanin sa ba, hkn yasa ko gaida shi taqi tayi dan kar ya balbaleta gaban qawar ta. Dashi har malika kallonta suke har suka shige, malika ta kalli mohd ta6e da baki tace"my man lokaci fa yayi da zaka gargad'a mana yrnyr nn, jifa har da wani kwashe kwashe take maka ,mohd yace"zanyi maganin ta ne ai ,in ni sa'anta ne ko kuma gidan nawa an gaya mata qwai da dunge duk shigowa suke suyi abinda suka ga dama"hm rainaka tayi wlh ita d'in kanta wace ce da har zata yo maka wani jajube jajube. Su Rynt kuwa har suka shiga d'aki gabanta na dukan uku uku . Byn ta nunawa wacce suka shigo tare bathroom tayo fitsari ta fito take ce ma Rynt "nikuwa Rynt ba mai gidan ki bane ya dawo?Rynt tace"shine" tace"ikon Allah sae kikayi kmr baki sanshi ba,"uhm"cewar Rynt yayinda er makarantar tasu bata sake cewa komai ba ta fita had'e da yiwa Rynt godiya. Nn kan saukowa upstairs ta had'u da mohd ta gaida shi ya amsa ba yabo ba fallasa snn ya wuce sae d'akin Rynt wacce ya samu ta cire niqab d'inta kenan ,tana had'a ido dashi tasha mai toka, shima fuskar sa tamau yake cewa "wace ce kika shigo min da ita a gida?tace"qawata ce" da wane dalilin ta shigo min gida? Lalura, shine kad'ai abinda tace ta kuma kama hanya zuwa bathroom haka shima bai sake cewa komai ba ya fitawar sa, fasa shiga batroom d'in tayi don dama tsoron kar ya dake ta yasa tayi niyar shiga bathroom,shiyasa ma tayi mamakin ganin ya fita bai yi mata fad'an ftr ta ba da kuma inda ta fito,ko meyasa,oho. Da dare mohd ya dawo daga masallaci sllr isha'i ya tafi d'akin malika ya sameta kwance tana waya tayi saurin katse wyr ta tashi ta tarbo shi cike da kisisina tace"ya akayi my man ko wnn abar ce takai ma koina don naga fuskar ka kmr ba annuri ,yace"yunwa ce wlh na rasa ina d'an iskan kukun nn ya shiga ace tun d'azu da muka dawo bai kawo mana abinci ba kuma har yanzu ba alamar za'a kawo,,tace"oh no am sorry my man ai baya nn, ina yaje? Wlh nice na sallame shi da zamu tafi honeymoon ,da sauri ya kalleta snn yace "meyasa? tace"me zai xauna yi to tunda bama nn" yace"haba malika mami fa? tace "naga fa a gabana ka damqa kulawar mami a gun yayanta nasir kuma kasan komai mami ke buqata nasir ba baqonta bane zata gaya mai kuma zai mata tunda ko baka bashi kulawarta ba ai dole ya kula da ita tunda qanwar sa ce,,kuma ai tun lokacinda mukayi tafiyar nn kullum a gida mami ke yini ko ba haka naji kana waya da shi nasir d'in ba?naji hkne ,kira shi kukun yazo ya dafa mana abinda zamu ci da daren nn don nikam ina buqatar naci abinci kafin na kwanta, to my man amma don Allah zanso na roqeka wani abu, fad'i inajinki,dama ina son naje gida ynz zuwa qarfe goma sae na dawo kaji, ya shafo cikinta tare da fad'in"to ki bari idan kinci abinci ko"um um lokaci zai tafi kuma idan naje gida ai zanci,to shike nn kira min kukun ni yazo ya dafa min nawa, tace"ok"snn ya fita. Yana nn kwance a d'aki ta shigo cikin shiri na qananan kaya amma ta d'aura after dress akai sae zuba qamshi take kallon ta yake har ta qaraso inda yake kwance kan sofa ,ta duqa gab dashi d'auke da murmushi a fuskarta takai bakinta kan nashi ta had'e,inda cikin minti 1 ta zare bakinta tana mai fad'in"ur food is ready sae kaje kaci then ni zan tafi "yayi murmushi yace"ok ki gaida su mama"tace"zasuji" snn ta fita. Shi kuma mohd ya fito ya nufi gun dining ya zauna har zai fara cin abinci sae kuma ya tashi ya nufi d'akin Rynt, Kai tsaye Rynt ta ganshi amma hkn bai hana tayi saurin 6oye littafanta na islamiya ba da ta ftr tana d'an dubawa,snn ta kalle shi kmr marar gsky ga hannyenta takai baya tana qara 6oye littafan a bayanta. shaye da toka yace"lafiyar ki? tayi saurin cewa"lafiya ba komai" ya qara shan mur snn yace"da bama nn a ina kuke samun abinda kuke ci keda mami? Tace"ina dafa mana ne kullum" to ina mami take ne yanzu?tana gida har yanzu bata dawo ba"yace"shike nn amma ki sani daga yau kar na qara ganin kucakar qafar ki a kitchen"ta gyad'a masa kai kawai shi kuma ya fita sae kawai ya had'u da mami ta wani maqalqaleshi tana mai murnar ganin shi. Washe gari da qarfe biyu Rynt tayi shirin ta tsaf na islamiyya ta fito cike da tunanin yanda zata kaya da mohd idan ya ganta. koda ta fito gate d'in gidan sae ko tayi kici6is dashi zai kunna hancin motar sa a cikin gidan. Yana ganin ta ya fasa shiga gidan sae ma tsaida motar sa da yayi ya fito,a lokacin Rynt jin tayi kmr ta kwasa aguje kafin ya qaraso gareta amma hkn ta dake tayi tsayinta har ya qaraso gab da ita har ma tana jiyo qamshin turaren shi. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:19PM, 1/25/2017] Ummi Ya: [1/18/2017] 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 🔮🔮🔮 _*page*_ *```30```* Taja baya da sauri tana fad'in"dan Allah kayi haquri ka barni na ci gaba da zuwa islamiyyar nn" tsaki yaja yace"kinga ba wnn ba abinda nake son sani shine kin gyara min d'akina ko kuwa? wane d'akin kuma,what!bangane wane d'akin ba kina nufin mami bata gaya miki saqona ba tun da safe? tace"bata gaya min ba"yace"to ai yanzu na gaya miki sae kije ki gyra min"badai yanzu ba kam don ni islamiyya zan tafi,yanzu kuwa er rainin wayo idan ba haka ba daga yau ma kin daina zuwa islamiyyar gabad'aya! Kmr zatayi kuka ta yaye niqabinta tana kallon shi tace"kayi haquri wlh in na dawo zan gyra maka,ke kina hauka ne da Allah koma daga ciki kije ki gyara min d'aki bana son wani shirme,tace"bafa wani jimawa mukeyi ba da qarfe hud'u muke tashi"ok so kike na zauna har qarfe hud'u banje d'aki ba,ko kuma so kike na shiga d'akin da datti. Kayi hqr kaje d'akin mtrka har in na dawo" kallonta kawai yayi ba tare da yace mata komai ba ya shigewar sa mota" Rynt ta sauke niqabinta ta kama hnyr islamiyya dmn abinda ta fhmta da kallon da ya mata yana nufin ta tafi. Mohd kuwa yana shiga gidan ya parker motarsa ya nufi cikin gidan bai zarce koina ba sae d'akin malika ya samu ummarta tazo. Sae bayan sun gama gaisawa snn ya fito yaje falon downstairs ya zauna zaman jiran dawowar Rynt nn ne ya ciro laptop d'insa yana wani aiki sae ga kuku ya kawo mai abinci yace"no bana buqatar abinci yau fruits kawai nake buqata kuma sae idan nayi wanka tukun, "ok sir"cewar kuku snn ya kwashi abincin ya mayar. Koda Rynt ta dawo ta same shi still zaune a falo sae aikin gaban sa yake,tayi kmr ma bata ganshi ba tasa kai zata wuce yace"ke zo nn" ba musu taje" yace"Kin raina ni ko? Tace"me kuma nayi"yace"kin sani zaman jiranki kuma shine kika shigo kmr ma baki ganni ba har kike qoqarin ficewa sbd tsabar raini ko,tace"to......shiii! bana son jin komai,je kawai ki gyara min d'akina ,kuma ki tabbatar kin fara da bathroom,tace"to idan nayi sallah zanje"ta fad'i hakane tare da Kama hnya zata wuce d'akinta, ya daka mata tsawa yace"wlh kafin na dawo masallaci na same ki a d'aki na na gaya miki"daga haka ya tafi zuwa masallaci ita kuma ta tafi d'akinta. Tana gama sallah ta nufi d'akin shi ta fara wanke bathroom kmr yanda ya buqata don tasan meye bathroom sbd tanaji a bakin mami. Ta fito snn ta fara gyra mishi bedroom ya shigo d'akin shaye da toka yace"kin wanke bathroom d'in ?tace"eh"yace"oya fita nn da minti d'aya sae ki dawo"ba musu ta fita shi kuma ya cire kayan jikin shi ya sanya white bathrobe ya nufi bayi. Koda ya fito daga wanka ya samu har ta gyra koina tsaf har ma tana batun fita yace"ke dawo ciro min kayan da zan sa"da sauri ta kalle shi sbd jin zancen sa wani iri ta dae basar tace "a ina kenan?bai yi mata magana ba sae nuna mata wardrobe da yayi ,ta nufi wardrobe d'in cike da tunanin ta ina zata bud'e don bata san kanta ba asali ma bata ta6a ganin irinta ba ko a film. Hkn ta dake zata kai hannu a jikin wardrobe d'in kenan sae kawai taga wardrobe d'in ta bud'e da kanta ta hnyr sliding, ai kuwa Rynt ta saki ihu tare da ja baya ,sae tsaki taji mohd yayi yace"bagidajiya kawai! ni je ciro min kayana kar ki 6ata min lokaci. Kmr zata yi kuka tace"kayi hqr bazan iya ba inajin tsoro". Tsaki ya koma yi yaje ya ciro kynsa da kansa snn ya danna wani abu a jikin wardrobe ta rufe duk Rynt na tsaye na kallon shi ya juyo yace"malama ai sae ki tafi ko?kmr dama command d'insa take jira ta fita abinta. Fitowar ta kenan ta had'u da malika zata raka mahaifiyarta ,yi tayi kmr ma bata gansu ba tayi ficewar ta. Mhfyr malika tace"me zan gani haka ita wace ce da har zata je 6angaren mijinki?malika ta ta6e baki snn tace"umma ai itace er matsiyata nñ wacce nake gaya miki Abbansa ya tilasta masa ya aura........ Iyye cabd'i zafa ayi er iskar yrny jibi fa yanda ta wuce mu kmr ta had'u da wasu gumaka ko wata gaisuwa babu, to umma me zakiyi da gaisuwarta ma nikam,mhfyrta tace"ba wnn ba ma me takeyi a d'akin mijin naki byn kince ba sonta yake yi ba? Ita ke gyara masa d'aki daman....... Kul! kar ki koma yarda ta shigar miki d'akin miji,kina hauka ne da baza ki gyara masa d'akin da knki ba,ni gsky umma bazan iya...... kwa6e mata baki mhfyrta tayi snn tace"ai kuwa in kika ce lalaci kina sake da baki zata qwace miki mijin,ni kinga tafiyata. Daga haka ta fita malika tace"wae tashin bomb ai ko sama da qasa zasu had'e tayi kad'an wlh!hm umma kenan ai ruwa ba sa'an kwando bane. Nn dai ta wuce sae d'akin mohd ta same shi yana sanya kaya tace"wae sae yanzu kayi wanka " ,to ba kin share ni ba wae ke umma tazo ,to my man umma ce fa, yace"ko ba umma bace hlnki ne idan kika yi baqi sae ki shareni, hm my man kenan kaida ba yaron goye ba har wata kulawa zan maka da baza ka iya yiwa knka ba,kallonta kawai yayi yace"jeki ga kuku nn a bakin qofa" Da yake dama duk wanda zai shigo 6angarensa yana sane don yana gani a jikin na'urar sa da ya saita. Malika taje ta bud'ewa kukun qofa tace"ya shigo" Wani qaton bowl ne kuku ya shigo dashi cike tap da 'ya'yan fruits kyace wani basarake ne zaici. Byn ya ajiye ya fita malika ta d'auki Apple d'aya tana ci,mohd dake kallonta yace"tashi ciro min freshmilk a fridge "taje ta d'auko tana mai fad'in "hln dae baka ci abinci bane my man? Yace"ina zaki sani to"shiru ta mishi dan ta fhmci yau kmr baya in gud mood. Bayan wata d'aya da faruwar haka kullum kuwa Rynt na zuwa islamiyyarta mohd baya hanata,sae dai duk zata tafi islamiyya in ta had'u da malika a falo sae tayi ta gaya mata maganganu marasa dad'in ji har da su zagi,ta uwa har ta uba duk don Rynt ta tanka ta,amma ko tak Rynt bata ce mata asali ma a marar tarbiya take kallonta. Mohd ne shida malika suna zaune a balcony sae firar su suke cike da nishad'i. Nan suka hango Rynt ta dawo daga islamiyya mohd ya duba wrist watch d'in shi 4:30 yace"me yarnyr nn ta tsaya yi har 4:30 bata dawo ba sae ynz" malika tace"au kai yau ka fara gani kenan,ai kusan kullum haka take bata dawowa kan lokaci kuma har rnr da ba'a zuwa islamiyya,fita take, what!har rnr da ba islamiyya fita ke?ta6e baki tayi snn tace"hm to kana da tabbacin ko ranakun islamiyya ,islamiyyar take zuwa ne,kullum ace bata ta6a tsallake lokaci ai ko nn abin dubawa ne,kuma ni abinda yasa tun farko ban gaya ma ba sbd kace baka so ina maka zancenta, mohd yace"dani take zancen"nn ya tashi ya nufi d'akin Rynt,koda yaje ya samu har ta fara sallah hkn yasa ya fito. Washe gari ta kasance rnr alhamis ba islamiyya gashi mami bata gidan tana gidan pretty ta kai musu yawo, Rynt kuwa ba inda take son zuwa irin gidan inna amma tunanin yanda zata tunkari mohd take. Har dai akayi sllr zuhur tana tunani akai da ta gama sll ta yanke shawarar zata fita idan ta ganshi ta tambayeshi ko Allah zai sa tayi sa'a. Koda ta fito kuwa yana nn zaune a falo sae dai shida wani abokin sa ne, ta juyawar ta zata koma d'aki yace"ke zo nn" Tana isa gurin su bata iya ko gaida su ba yace"dama kuwa an gaya min fita kike har rnr da ba'a zuwa islamiyya, shine yanzu kin fito kika ganmu kika koma sae idan mun tashi sae ki sake fitowa ko?cikin rashin fhmta Rynt tace"nifa ba fita zanyi ba kawai na fito ne na tambayeka ina son zanje gidan inna sae na ganka tare da baqo" qarya kike yawon iskancin ki dai ya fito dake, yawo kuma nida koina bana fita sae zuwa islamiyya,yau d'in ma islamiyya ta fito dake kenan? Gidan inna fa nace maka zan tafi....wace innar byn kullum sae ta tasani gaba na baki wayata kuyi waya! cikin muryar kuka tace"to ai waya daban yanzu ina son zan ganta ne.....to ba inda zakije don haka koma daga ciki! Uhm Uhm dan Allah.....ya tashi daga zaunen da yake had'e da daka mata kafurar tsawa har sae da hawayen da suka cika mata ido suka sauko ba shiri, yace"ki wuce nace! Jiki ba qwari ta koma d'aki tana kuka. Shi kuma ya buga tsaki ya koma ya zauna . Abokin sa yace"ya kana dakawa mace tsawa haka,irin haka idan tana d'auke da juna biyu ai sae ya zube,wani mugun kallo mohd ya watsawa abokin nasa snn yace"wane uban ne zai mata juna biyu, to kaddai ka zage ni abu mai sauqi kawai ka sallami ynyr nn ni na samu na aureta don wlh tayi min,da takaici mohd ya sake kallon abokin nasa, abokin yace"to wae naga baka sonta ni kuma da Allah ya hore min sonta ba sae naji da ita ba"mtsw ga dukkan alama sae da kasha ka zo min gida"eh kam amma kafi kowa sanin ni na daban ne don nasha bashi zai sa na fita hayyacina ba,to ka cire sonta don wnn ba mtr aurenka bace, hhhhh wae don tana mtrka hm kamanta waye ni kenan, ko d'aya kawai ba mtr aurenka bace kmr yanda na fad'a ma, ko meyasa?sbd talaka ce er matsiyata shiyasa sam bata cikin tsarina kuma kai nasan ma zaka fi tsanar ta akaina....ai har sonda nake mata ma ya koma tsana don kasan ba abinda na tsana a duniya kmr talaka kuma su da kiyashi duk d'aya ne a gurina sae na taka su na wuce ba komai bane,amma kai ya akayi har ka aureta? Abba ne wlh, wae ya tilasta maka? Eh, hm abinda bazan ta6a d'auka agun iyayena ba kenan,don sun haifeni bashi zaisa su tilasta min kan abinda bnyi niyya ba wlh, gsky Abba ya cuceka,mohd yace"abinda umma ke fad'a masa kenan, wacce tun lokacinda nayi auren nn take fushi dani,nayi vata haquri har ngji tace idan ina son ta hqra sai idan na rabu da wnn yrnyr ko zata janye fushin....mtsw amma kuma shine kake tare da ita har yanzun,hm ina kan hnyar rabuwa da ita amma tsinuwar Abba nake yiwa gudu.... Ya tsine maka man sae me, ai ba akan ka aka fara ba,hm jamil kenan gwanda dai ka rabu da iyayenka lfy shi yafi,kaji matsalarka kullum biyayya wa iyaye ai gashi ka fara ganin illar hkn ansa ka auri mata har biyu kmr wani bagidajen mutum,murmushi kawai mohd yayi yayinda abokin nasa ya tashi yana fad'in"kaga ni sae anjima dan bazan iya zama ina jin wnn takaicin ba. Bayan kwna d'aya da faruwar hkn rnr ta ksnce rnr assabar ,Rynt tayi shirin ta na islamiyya tsaf ta fito zata tafi ,a nn falo tayi kici6is da mohd shida malika da suka lula duniyar romance ,da sauri ta kauda idonta zata fita, mohd ya dakatar da ita,ta tsaya ba tare da ta juyo ba ya taso tare da fad'in "ina kuma zuwa?tace"islamiyya mana zan tafi,to na soke islamiyya daga yau!da sauri ta kalle shi tace"meyasa? Malika ta taso tace "amma fa ta rainaka har tmbyr ka takeyi ,yace"ubanta ta raina bani ba,kuma daga yau duk na qara yanke miki hknci kika tambaye ni dalili ni nsn hnkncin da zan miki,snn daga ynx kar na qara ganin kin tako qafar ki a falon nn...kayi dai dai my man don kullum ba abinda nake ji maka tsoro irin kar ta kwaso ciki gurin baqin yawonta azo ace naka ne tunda kaine mijinta,ko yanzun dai Allah ya tsare idan ba a riga an kwason ba, tunda kullum gata nn cikin hijabi kmr wata tsohuwar malama, Rynt ta kalle ta da kyau snn tace"Shi wanda ya haifeki d'in ma har ya kasa baki tarbiya bai isa yamin ciki ba bare har ayi tunanin laqawa wani banza can". Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:19PM, 1/25/2017] Ummi Ya: [1/19/2017] 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 🔮🔮🔮 _*page*_ *```31```* Malika tayi tsaye sororo sbd tsananin mamaki,mohd kuwa kallon Rynt yake kmr wanda yaga abin burgiewa a tare da ita, sbd a cikin kwanciyar hnkli ta saki mgnr kmr ma ba ita ba. Rynt kuwa na gama fad'ar mgnr ta juyawar ta zuwa d'aki ,sae a lokacin malika ta saki wani irin zagi ta tafi fuuu!tabi Rynt tana fad'in"cabd'i lallai yau sae kinsan wa kika ta6o,har ni zaki zaga ki kwashe lfy! Koda ta isa d'akin Rynt tuni Rynt ta rufe d'akinta tasa makulli ta kuma je tayi kwanciyarta akan bed, malika ta shiga sirfa bala'i tana dukan qofa kmr zata 6alle qofa, duk Rynt na jinta tayi banza da ita. Mohd ne yazo yaja malika yana fad'in"don't mind her xo mu tafi kawai"tace"banni da er iska tambadaddiya idan ba tsoro ba ta fito mana,wlh ta fito!taga yanda ake quliqulin kubra da mutum. Da qyar dae mohd ya samu ya jata suka bar gurin . 2 days a go Kwata kwata mohd ya daina zuwa d'akin Rynt dmn zuwa duba lfyrta kmr yanda Abbansa ya tilasta mai, haka kuma bai qara ganin ta fito ba, sam bai damu ba sbd a cewar shi dokar da yasa mata ce tabi. Malika kuwa tun a rnr da abin ya faru tayi tafiya da yamma zuwa garin kd gun bikin wata qawarta yayinda ta tafi d'auke da alwashin duk ta dawo sae tayi ma Rynt dukan ftr hnkli. Kwance yake a falo shi kad'ai yana hutawa sae ga mami tazo ta same shi tace"dan Allah yaya ina son naci chocolate"sae da ya kalleta snn ya tashi zaune tare da zaunar da ita kusa dashi yace"to bari na byr a siyo miki"um um yaya inada shi a d'aki amma hannu na bazai kai inda Anti ta ajiye min ba, to kice Antin ta d'auko miki mana, ai bazata iya bane, meyasa bayan ita ta ajiye? Anti bata da lfy fa, ko abinci ma ta daina ci,kullum sae kuka take tayi ,gashi kai baka zuwa kullum bare ma kasani ynx haka ma tun dazu take son ta tashi amma ta kasa sbd jiri ke d'ibar ta"man yayi shiru yana kallon mami can yace"naji jeki zanzo na duba ta. Ya jima kafin yake zuwa d'akin don koda ma yaje ya samu har mami tayi bacci sbd dama dare ne, ya sami Rynt zaune kan bed ta had'e kai da guiwa,sallamar sa yasa ta d'ago wanda kallo d'aya ya mata ya fhmci tana jin jiki, fararen idanuwnta duk sunyi jajir yayinda eyelashes d'inta sukayi warawara sbd hawayen da suka ta6a su , snn fuskarta fayau ba kwalliya kmr kullum,maida kanta ta koma yi tsakiyar qafafuwanta shi kuma yaje kusa da ita ya zauna kan bedside drawer yace"me yake damunki ne?tayi shiru kmr bata jinsa yace"kina jina fa"tace"nima ban sani ba"yace"to ki shirya zan miki allura ne"tace"bana so"baice mata komai ba sae tashi yayi yabar d'akin,Rynt kuwa sae tashi take sonyi amma ta kasa sbd jiri wacce dama idan tana zazza6i haka yake mata. Can ta samu ta tashi tsaye se kawai jiri ya d'ebe taje zuwa fad'uwa,bata fad'in ba sae jin tayi an kamata, a firgice ta juyo tare da fad'in"baffa"sae kawai taga ashe mohd ne riqe da ledar magunguna a hannun shi, wani irin baqinci taji don ta d'auka ko Baffanta ne ya dawo gareta kmr yanda take mafarki a kowane dare,hawaye ne suka zubo mata bata damu da ta share ba sae jaye jikinta daga nashi tayi snn ta koma ta zauna, mohd kuwa ya d'aura ledar magunguna kan bedside drawer yaje ya d'auko gorar ruwa da cup snn yaje ya zauna kan gadon tare da tsiyaya mata ruwa a cup, ya bata ta kar6a shi kuma ya shiga 6alle magunguna ,ya bata taqi kar6a sae ruwa takai a bakinta tana sha, tayi saurin ajiye ruwan sbd wani irin abu da taji cikinta nayi na rashin abinci ga ruwa ta kora akai, nn take taji amai ta yunqura zata tashi amma jiri bai barta ba tayi saurin dafa kan gadon gudun kar ta fad'i, mohd yakai hannu zai taimaka mata, tayi saurin dakatar dashi ta hnyr cewa"bana so"bai kula ta ba sae janta yayi suka tafi bayi don ya fhmci gab take da kwaro aman, suna shiga ta warce hannunta daga nashi ta dafa washbasin tana kwara amai a ciki,kalar aman ya soma tsorata mohd yace"ke wnn aman fa? wani kallon takaici ta watsa mai tare da fad'in" juna biyu nake d'auke dashi ko da wata matsala ne! d'an shu'umin murmushi mohd yayi tare da kauda kansa gefe nn idon sa ya hango masa bayan hijabin Rynt da yayi staining da jini, yakai hannu ya riqo hijabin ya nuna ma Rynt snn yace"ya haka kuma keda ke d'auke da juna biyu sae na sami wnn qazantar a hijabinki ko kuma jin ciwo ne? Kunya Rynt taji sosai tayi saurin kauda kanta tare da fizge hijabinta ta 6oye gurin da yayi staining,murmushi yayi tare da fita bayin. Hannu takai kan mixer tap ta kunna famfo ta kuskure bakinta ta wanke washbasin taje a daddafe ta saka key a qofa snn ta cire hijabi har kayan jikinta, ta saka su a bucket ta zuba ruwa da klin bata iya wanke wa ba sae wanka tayi koshi da qyar taga ta samu ta kammala ta d'aura towel ta fito toilet corner ta jawo qaton hijab d'inta har qasa ta zuba snn ta fito,ta sami mohd zaune yana jiran fitowarta wanda baiji fitowarta ba sae qamshin sabulun da yaji sosai hkn yasa ya d'ago ya ganta,ya tashi tare da fad'in "idan kin shirya zan dawo"bata bar sun had'a ido ba ta kauda kanta gefe har sae da taji ya fita snn ta nufi wardrobe ta shirya taje tayi kwance tare da jan blanket ta rufe jikinta har kanta, sae ga mohd ya shigo d'akin d'auke da freshmilk da kuma plate d'in abinci don ya fhmci aman da tayi na yunwa ne. Yaje tare da ajiye abincin kan bedside drawer snn yace"ga abinci nn kici snn kisha magani" Nn ya juya zai bar d'akin tace"ni bana cin abinci ka koma dashi" Ya dawo tare da fad'in "dolen ki kici don ba ajiye ni kikayi ba da zan kawo maki abu na koma dashi" Nn ya tilasta ta kan dole ta tashi zaune, ya dungura mata plate d'in a jikinta ,takai hannu ta ture plate d'in tace"nifa na gaya ma bazan ci ba" kallonta kawai yayi bai ce mata komai ba sae hannuwan rgrsa da ya shiga linkewa shaye da toka yayinda Rynt ke kallon sa da mamaki kaddai d'ura mata abincin zai yi ta qarfi,tana kallo ya d'auki plate d'in ya d'ibi abincin a spoon ya nufo bakinta dashi kmr zatayi kuka tace"nace maka bana so dan Allah ka barni"daga nn kawai ta fara kukanta a hnkli ba don komai ba sae don tuna baffanta da tayi wanda sam baya takura ta akan komai. Haqiqa tayi rashi babba wanda har abada bazata sami kmr sa ba. Tayi minti biyar tana kukanta mai ban tausayi mohd sae kallonta yake wanda ga dukkan alama ta fara bashi tausayi ,a hnkli ya sauke numfashi snn yace"idan kinci zan barki ki koma islamiyya kuma zan barki kije gidan inna"da sauri ta kalle shi snn tayi magana cikin muryarta ta marasa lafiya tace"dagaske kake?ya gyad'a mata kai snn takai hannu takar6i plate d'in abinci tana mai kallon shi tace"ka tafi kawai zanci" ba musu ya tashi ya fita don ya fhmci bata iya cin abinci a gaban idon sa ne. Sae da yayi wanka ya kuma yi shirin bacci snn ya dawo d'akin ya samu taci abinci kmr yanda tace ta kuma sha duk wasu magunguna da ya 6alle mata,yakai hannu ya d'auki plate wanda ke d'auke da ragowar abinci snn ya kalleta sae sharar baccin ta take cikin natsuwa. Wayar sa ce tayi qara ya saka ta a silent snn ya d'aga had'e da fita d'akin. Washe gari Alhmdlh jiki ya fara yiwa Rynt sauqi don da taje wanka har kayan da ta jiqa cikin bucket jiya ta wanke abinta tas taje ta shanya. Byn ta shirya snn tayi breakfast ta koma ta kwanta sbd zazza6in bai qarasa sakinta ba,ba jimawa bacci ya kwasheta sae ga mohd ya shigo d'akin riqe da hannun mami,yaje kan bedside drawer ya zauna mami kuwa ta hau kan gadon tana fad'in"anti ma tayi bacci" Komai mohd bai ce ba sae hannun sa ya d'ora kan goshin Rynt,sae kawai yaga ta bud'e idanuwanta a hnkali ta sauke su akan nashi, ba tare da ya sauke hannun sa da ke kan goshinta ba yake tambayar ta "jikin fa? Billy giro 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:19PM, 1/25/2017] Ummi Ya: [1/20/2017] 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 🔮🔮🔮 _*page*_ *```32```* Shaye da toka ta janye hannunsa snn tace "Alhmdlh" Shi kuma ya màida dubañsa gun mami yace"bani ruwa gasu can a bayanki kan bedside drawer, mami ta kawo mai ruwan ya kalli Rynt da tun d'azu ta juya bayanta dmn ci gaba da bacci,yace"tashi kisha magunguna idan ba haka ba ciwon zai sake dawo maki ne" Ba musu ta tashi zaune ,har zai 6alla magungunan sae kuma ya kalleta yace"ko kina so na had'a miki da allura sbd naji jikin naki da zafi kuma zaki fi jin sauqi a take"kallon sa tayi ,sae kuma tayi shiru don dai tana son samun sauqi nn take kam ko don zuwa islamiyya ta kuma samu taje gidan inna, amma bata jin zata iya bashi wani guri a jikinta ya mata allura,cikin sanyin murya tace"Aa bana son allura zansha magani kawai" Bai musa mata ba ya bata magungunan tasha, snn ya tashi zai fita,mami tace"nazo mu tafi yaya"yace"Aa mami asibiti zan tafi"tace"yaya ina zuwa ko can d'in ne"yace"mami idan yawo kike so bari gobe zaku fita keda Anti kinji"yaya to ai anti bata da lfy kawai wayo kake so kamin"ta qarashe mgnr ne kmr zatayi kuka yace"zo" tazo gurin shi ,ya rage tsawon sa tare da kai hannu ya shafo fuskarta yace"kar kiyi kuka ba wayo nake miki ba dgske nake zaku tafi yawo gidan inna idan anti taji sauqi kinji"to yaya haka ko jiya da dare nayi ta jiranka kazo ka d'auko min chocolate har nayi bacci baka zo ba"eyyah mami ai kina ficewa aka sallama min sae ya kasance koda na dawo na samu har kinyi bacci amma yanzu nuna min inda chocolate d'in yake sae na d'auko miki ko"hannunsa taja tana fad'in "muje kaga ai a wardrobe d'ina ne amma can sama, nn ta bud'e wardrobe d'inta ya d'auko mata ya vata, ta kar6a cike da murna shi kuma ya fita, Rynt dake kallon su sae mamaki take irin yanda yake shiri da mami amma kaf sauran qannan sa tsoronsa suke ji. A washe gari ne mohd ya cikawa Rynt alqawarinta yakaita gidan inna ita da mami suka yini sae dare ya maida su. D next day Rynt ce a d'akin mohd tana gyara mishi d'aki sae ga malika ta shigo d'akin wacce saukar ta kenan, wani irin farin ciki ta sami kanta dashi ganin Rynt a d'akin,ta rufe qofa da makulli ta kuma cire makullin ta jefa a jakarta a cewar yau ko ita ko Rynt dole ne a kwashi gawar d'ayan su,sae da tayi d'amara snn ta shiga dube dube taga ko zata sami wani makamin da zai raba Rynt da duniya zama d'aya ,can taga tunda ta rasa makami , abnda yafi kawai taje da qarfin tsiya ta kwashi qafafun Rynt ta yanda idan takai qasa sae dai wata ba ita ba. Tana gama yanke shawara ta nufi Rynt gadan gadan wacce sam bata san da shigowar malika ba sae aikin gabanta take,ai kuwa kai tsaye taji an kwashi qafafunta kafin takai qasa ta buga ihu cike da mugun jin tsoro,malika kuwa a maimakon taga Rynt qasa sae ganin ta tayi a jikin mohd,wani baqinci ne ya tokare ta a wuya ganin Rynt male male a qirjin mohd sae baqin ciki biyu suka tara mata,cikin azama ta ciro takalmin ta mai d'an karan tsini zata dokawa Rynt shi a ka mohd ya riqe mata hannu da d'ayan hannunsa sbd d'ayan hannun yana rungume da Rynt ne wacce tuni ta some kan tsoratar da tayi,ya fizge takalmin had'e da daka mata tsawa yace"meye haka,me ta miki keda yanzu ne dawowar ki!bata kula shi ba sae d'ayan takalminta ta ciro tana fad'in"cabd'i har ka manta zagin ubana da tayi kenan,wlh yau sae tasan ba irin mu ake zagi a zauna lfy ba!tsaki yayi ya sake fizge takalmin ya kuma ture ta, tayo kukan kura ta ture Rynt daga jikin shi, nn Rynt ta fad'i kanta ya daki gefen gado,bata barta ba tayi kanta zata fara kai mata duka,mohd ya rirriqeta ta shiga kokawa dashi na ganin ta qwace kanta,bata iya qwatar kanta ba sae mohd d'in ne yaga dama ya saketa tare da fad'in" can't u see she is unconscious,to bari kiji wlh duk kika ta6a ta zanyi maganin ki ne kuma ki gwada ki gani kin dai san hali na ba sae an gaya miki" Tace"wlh ko ba yau ba sae na hallaka ta kuma bari ka gani kul ba dad'e kul ba jima kuwa" Daga nn taje ta bud'e qofa ta fita sae masifa take tayi. Mohd kuwa d'aukar Rynt yayi ya d'ora ta kan bed, snn ya samo ruwa ya shiga yayyafa mata a fuska, cikin ihu da firgici ta tashi ta qanqame mohd tana karanto addu'o'i sbd duk d'aukar ta aljanu ne suka cirata sama,duk tabi ta firgice tana ta mai kuka,ya qara rungume ta a jikin shi yana kwantar mata da hankali,sae can ya samu hnklinta ya d'an fara dawowa gareta,inda a hnkli yaga takai hannu kan gefen goshinta gurin da kanta ya daki gefen gado, ta d'ago hawaye tap a idonta tana kallon shi,yace"da zafi? tace"wlh d'akin nn naka aljanu ne dashi kaga har sun jimin ciwo"kallonta kawai yake bai ce komai ba sae hannun ta ya janye yana duba gurin, gurin yayi ja har ma yad'anyi lolo kad'an, nn ya lumshe ido tare da shirin maida ta kan qirjinsa had'e da cewa "sorry". Cikin tsananin mamaki da jin haushi ta kalli abinda yake shirin yi don sae a lokacin hnklinta ya gama dawowa jikinta,ai kuwa tayi saurin hana faruwar hkn ta tashi da sauri zata bar gadon ,by mistake hannunta ya latsa wani guri a jikin gadon abin mamaki da ban tsoro a gun Rynt sae kawai taga wasu silalan fararen qarafe na fitowa kowane gefe ta jikin gadon,ihu ta saki ta sake komawa jikin mohd ta qanqame shi amma ta kasa d'auke idon ta akan abinda ke ci gaba da faruwa don wani farin qyalle tagani shar shar kmr net yana biyo ta jikin qarafen har ya lullu6e su sae gadon ya zama kmr suna cikin wata kyakkyawar rumfa ne mai kyan gaske. Kuka ta fashe masa dashi tace"wlh na gaya ma d'akin nn aljanu ne dashi dan Allah ka ftr dani ,na roqe ka" Kallon ta mohd keyi yanda ta rud'e sosai tana kuka don jikinta har qyarma yake,yakai hannu ya danna wani guri a jikin gadon sae kawai komai ya shiga komawa a hnkli har gadon ya zama tamkr ba shine ya musu rumfa a d'azun ba. Ya kalli Rynt dake qanqame a jikin shi snn yace ni d'akina ba aljanu gidadanci ne kawai irin naki sae ki tashi ki fita duk kin wani cumuimuyen min a jiki haka"cikin kuka had'e da masifa tace ba aljanu amma d'azun aka kwasheni akayi sama dani"yace"wnn kuma ya rage naki nidai ki fita nace"tace"ai ko baka ce va ynxn fita zanyi" ta fad'i hakane kawai amma kuma bata iya sauka kan gadon sbd tsoron kar ta sake ta6a wani gurin, ganin haka yasa mohd ya saukar da ita, ta kalle shi shaye da toka snn tabar d'akin,cike da alqawri a ranta bazata qara tako qafar ta a d'akin ba. Haka ko akayi don tun daga rnr Rynt bata qara komawa d'akin mohd ba ,wanda yanzu an d'auki lokaci sosai don har su saliha sun dawo hutun makaranta suna batun komawa first term. Duk tsawon lokacin nn mohd shi ke gyara ma kansa d'aki sbd duk lokacinda ya aika mami Rynt taxo ta gyara mai d'aki sae tace bata jin dad'i. Malika kuwa takaici ma ne yace ta gyara mai d'aki don acewar shi in banda qara lalata mai d'aki ba abinda ta iya. Yau ya dawo a gajiye daga asibiti ga d'akin nasa yana buqatar gyara ya aika mami yace taje ta gaya ma Antinta tazo ta gyara mai d'aki ta dawo masa tare da saqon wae anti tace bata jin dad'i. Tashi kawai yayi ya tafi sae d'akin Rynt ya sameta zaune tana duba littattafanta na islamiyya sbd rnr,rnr alhamis ce basa zuwa islamiyya . A fusace ya d'auke littattafan ya d'aura su kan bedside drawer snn yace"bana son raini tashi kije ki gyara min d'akina! Shaye da toka tace"nifa bana jin dad'i"da Allah maza tashi ai baki zo nn gidan dan kiji dad'i ba!tace"nifa ina nufin bana da lafiya.....cikin mugun hasala ya nuna ta da yatsa yace"kar ki kuskura na koma jin wnn kalmar a bakin ki, yau wata kusan nawa kenan duk nace ki gyara min d'aki kice ba kya jin dad'i sbd kin raina ni ko shine har kike tunanin zan ci gaba d'aukar miki rainin,to bari kiji wlh duk baki je kin gyara min d'aki ba ,ba ke ba zancen bokon nn kuma ba wanda ya isa ya tilsatani na saki!daga haka ya fita kmr zai tashi sama, yabar Rynt qwallah cike tap a idonta tana tunanin in taje aljanun d'akinsa zasu iya sake cirata sama su yar wata qil ma wnn karon mutuwa zatayi ba suma ba, gashi kuma bokon nn tayi bala'in qwallafa ranta akai har kullum ma qidayar kwanaki take inda yau sauran ta kwana uku ta fara zuwa mkntr boko gashi har ma an d'inka mata uniform saura littattafai da takalmi. Tana cikin share hawayenta ne sae ga saliha ta shigo, tace"Rynt lafiyar yaya naga yaja mota a hasale ya fita! Rynt tace"Yauwa saliha tun da ya fita dan Allah taimakamin kije ki gyara masa d'akin sa...ke wlh ni bazan iya da halin yaya ba kawai kije ki gyara masa keda yasa,saliha bazan iya bane d'akinsa tsoro ake ban dan Allah ki taimakamin kije ki gyara masa kafin ya dawo wlh yace idan ban gyara masa ba bazan yi boko ba kuma kinfi kowa sanin yanda nake son nayi bokon nn"ta qarashe mgnr kmr zatayi kuka saliha tace"nifa fad'an sa nake yiwa gudu ba komai ba"Rynt tace"kawai kije ki gyara duk fad'an da zaiyi aini zai yiwa tunda bai san cewa ke kika gyara d'akin ba, shiyasa ma nake son kiyi sauri kafin ya dawo dan Allah. Da qyar dai saliha ta yarda ta tafi,wacce ta fara gyra masa d'akin kenan sae ga mohd ya shigo d'akin fuskar d'auke da 6acin rai sosai. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:19PM, 1/25/2017] Ummi Ya: [1/22/2017] 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 🔮🔮🔮 _*page*_ *```33```* Gabad'aya saliha ta gama tsorata da ganin yanayinsa,yayinda take roqon Allah yasa ta 6ace 6at kafin ya qaraso gareta. Mohd kuwa a fusace ya qaraso gab da ita sae huci yake yace"uban me kika zo yimin a d'aki !dake nake ki bani amsa!! A tsorace tace"yaya wlh qaddara ce amma don Allah kayi haquri wlh Allah bazan sake ba" Kunnen ta ya kama ya shiga yi mata fad'a sosai sae kuka take tana bashi hqr sae can ya sakar mata kunne yace"Oya fita na daina ganin ki a nn stupid gal!da sauri ta fita d'akin har tana had'awa da gudu,sae ga malika ta shigo d'akin wacce dama ita ce ta kira mohd a waya ta snr dashi cewa Rynt fa taqi zuwa ta gyra mai d'aki kmr yanda yace,sae saliha tasa a cewar ita ta gaji da gyarawa qaton banza d'aki. Dmn duk wani abu da ya faru na fad'an da mohd yaje yayiwa Rynt tana la6e,har ma lokacinda saliha tazo duk sae da taje ta la6e,shine fa ta had'e qarya da gsky ta gaya mai. Tace "wlh my man wnn abar ta rainaka da yawa amma ka kasa maganin ta na rasa meyasa,yace"ni kaina malika na rasa meyasa ta raina ni haka wlh! Hm my man maganinta ne bakayi shiyasa. Tsaki kawai yayi ya fita daga d'akin. Saliha kuwa tana fita d'akin Rynt ta nufa tana shiga Rynt tace"ya akayi ne saliha ko ya dawo ne? Komai saliha bata ce ba sae d'aukar jakarta tayi ta fita. Rynt ta biyota tana fad'in "saliha kimin bayani mana" sam saliha bata saurara mata ba tayi ficewarta. Ita kuwa Rynt tana kawowa bakin qofa tayi kici6is da mohd da qarfi ya turata ta koma ciki ya kuma rufe qofar da key. Inda kai tsaye ya yakai hannu kan wuyan hijabinta ya rabashi biyu, a firgice Rynt tayi saurin kama hijabin ta riqe tace"malam meye haka dan Allah! bai kulata ba sae hijabin ya fizge ya yar ,ta koma d'auka ta rufe jikinta. Sai kawai yaje yayi zaune abinsa kan sofa ya d'aura qafa kan qafa yana juya belt d'in hannunsa a hnkli snn ya kalli Rynt da taje jikin wardrobe zata nemo wani hijabin yace"ki ma daina wahaladar da kanki don kaf kayan jikin ki ne zan raba ki dasu sbd ni sam bana dukan mutum da kaya a jikin shi, ta fiddo ido waje cike da tsoro tace"kenan kai d'an iska ne"yace"eh sosai yanzu kuwa zan nuna miki"ya taso gadan gadan zai zo gurinta. Tace"Aa dan Allah kayi haquri wlh zanje na gyra ma d'akin ka indan shine " Idan na gama dukan ki ba ya fad'i hankane tare da fizge hijabinta ya jefar ya kamo wyn rgrta zai yaga...tace"wayyo dan Allah kayi hqr"ta qarashe mgnr tare da fashe masa da kuka tana roqon shi yace"shin saliha bata gaya miki horon da nake musu bane da suna en yara"cikin kuka sosai had'e da girgiza kanta tace"wlh Aa bata gaya min ba"yace"to kiji kaf qannai na duk wanda yamin laifin duka se ya cire tufafin sa nake dukan sa sbd ni ba sakaran mutum bane da zan daki mutum da kaya a jikin shi, kuma duk na daki mutum sau d'aya to ko da kuskure bazai qara min laifin da zan sake dukan shi ba, amma ke sbd a iya qafafun ki kad'ai na daka shine kika sake min wani laifin duka wae har ni zaki duba ki kira qaton banza,yana kawo nn sae jin tayi bata tare da rgr jikinta don zama d'aya ya yage ta ya jefar ,ya zamo vest kad'ai ke jikinta sae kuma zani ,wani irin kuka ta fashe dashi mai cin rai had'e da saurin durqushewa qasa,tana girgiza mai kai tana ja baya sbd yanda yake matsowa kusa da ita, cikin zafin nama ya miqar da ita tsaye tayi saurin sa hannayenta ta kare qirjinta tace"idan kai musulmi ne na roqe ka da girman Allahn da muke bauta ma kar ka rabani da kayan jikina"hannu yakai ya jaye tsorayen kalabarda suka soma rufe mata fuska snn ya d'ora hannayensa kan kumatun ta da hawaye keta fmn sintiri yace"na barki sbd girman fiyayyen halitta amma ki sani bake ba boko har abada! Nn ya juya ya fita ,ita kuwa taje kan bed cikin tsananin kuka taja blanket ta rufe jikinta har wuya nn ta had'e kai da guiwa tana ci gaba da kukan da duk wanda ya gani zai d'auka ko kaf duniya an mutu ita kad'ai aka bari a raye sbd baqin cikin yanda ya rabata da hijabinta har rgrta sae duk taji duk duniya ba wanda ta tsana kmr shi,sbd still cikin su ukun nn tafi yarda a ranta cewa shine dai makashin babanta. Qofa taji an turo tayi saurin d'agowa don ta d'auka ko shine ya dawo, sae taga malika ce wacce ke d'auke da shu'umin murmushi a fuskar ta tace"kad'an kenan daga cikin sharrin na,dmn ni ba'a taka ni a zauna dai dai,inace yanzu kin fara ganin kuskuren ki na auren mijin da ba naki ba,wanda kwata kwata ba'a halitto shi wa kowa ba sae ni kad'ai,amma sbd kwad'ayin duniya irin naki kika shigo sabgar da ba taki ba,kika lalata min tsarin rayuwata gabad'aya, to bari kiji wlh idan har bakiyi gaggawar rabuwa da mijina ba nice zan zamo ajalinki. Kmr bada Rynt take zancen ba don tun lokacinda Rynt ta d'ago taga wace ce ta maida kanta kawai taci gaba da kukanta,har kuwa ta fita. Har kusan kwana biyu Rynt bata bar kukan abinda mohd ya mata ba sbd taji ciwo sosai fiye da zaton mai karatu,dmn idan aka cire mutuwar mahaifinta to shine abu na farko da tafi jin ciwon sa a duniya. Duk kwana biyun nn mohd na shigowa d'akin Rynt da safe kafin ya tafi asibiti,wanda duk shigowar da yake ganin ta yake zaune kan bed ta had'e kai da guiwa kuma har ya fita bata d'agowa bare zancen gaida shi. Sallar zuhur ta gama snn ta tashi tayi shirin islamiyya ta fita. Bayan sun tashi da qarfe hud'u a maimakon ta koma gida sae napep ta nema ta tafi gidan inna. Mohd na zaune shida malika kan dining inna ta kirashi a waya sae masifa take mai, kan dole ya ajiye zancen cin abinci ya tafi gidan inna. Inna tasa shi d'aki shida Rynt tace"sae naji Rynt tazo min da wani zance wae ba zaka barta tayi boko ba,yace"bata snr da ke laifin da tamin bane inna.....Yo dan bata je ta gyara ma d'aki ba har shine wani laifin da za kace ba za tayi boko ba,to bari kaji ubanka kabiru ma bai isa ya hanata bokon nn ba bare kai,boko kam sae Rynh tayi shi kmr kowa don ba za'a barta a baya ba,kuma dolenka ka d'auki nauyin krtn tunda mtrka ce,yace"gsky inna kiyi hqr don na riga da yanke hukunci.....inna ta dunqule yatsu ta watsa mai tace"ubanka! nace ubanka kabiru! yo har ni zaka duba kace ka rigada ka yanke hknci sbd ban haifeka ba ko,ko d'aya ba hk bane inna sae fa da na gaya mata duk bata je ta gyara min d'aki ba bokon ta ne haka wae shine don ta raina ni ta saka saliha wai ita ta gaji da gyrawa qaton banza d'aki har ni zata kira qaton banza !Rynt tace"wlh Allah inna bance masa qaton banxa ba..... A fusace mohd ya taso xai bugewa Rynt baki, tayi saurin tashi ta koma bayan inna ta la6e ,inna ta tashi tace"yo da dukanta zakayi to"cikin yanayi na 6acin rai yace"to inna ni sa'anta ne da zata qaryata" inna tace" lallai Muhammadu sam albasa bata biyo hln ruwa ba indai kace dukan mace kake, don ubanka kabiru duk iya shegenda uwarka take mai bai ta6a sa hannu ya dake ta ba, kai kaf ubannanka ba mai dukan matar sa, sae kai zaka ce ka fara sbd baqin zuciya irin taka, nn ta maidà dubanta gun Rynt da ta soma kuka tace" zo zauna abinki ya dake inga inshi shashan yaro ne. Sae da ya koma ya zauna snn Rynt ta iya zama yace"inna ki barni kawai da yrnyr dan Allah ki ftr da bakin ki a cikin zancen nn......naqi na ftr d'in shashan yaro ai kwanaki kafin aurenka zowa kayi nn ka nemi na roqa maka alfarma agun mahaifinka don ka samu kaga ka auri wnn yrnyr er marasa mutunci ,shine yanzu tunda burinka ya gama cika har ni kake cewa na daina sako bakina a cikin zancen ka ,iye lallai Muhammadu yau ka nuna min ban isa dakai ba. Ta qarashe mgnr ne cikin muryar kuka irin nasu na tsafi d'in nn. Cikin nuna damuwa mohd yace"inna ba haka bane wlh yrnyr nn tafa ranani sosai wanda dole ya kamata ace na d'auki mataki akai......yo muhammadu ita Rynh d'ince ta rainaka yrnyr er albarka wacce ba ruwanta da kowa, kuma ai tunda na sako bakina a ciki ya kamata ka haqura koma mene ne idan kuma banda wani matsayi a gurinka shikenan sae ka tashi ka tafi ai inada kud'in da zan sata mkrntr ba wai rasawa nayi ba. Kauda kansa yayi gefe cike da takaici yace"ki barshi kawai zan sata d'in" inna tace"bama so! kuma idan kaje gidan naka ka aiko min da duk kayan Rynh don a nn zata zauna tayi bokon ta" Nan Mohd ya shiga ba inna hqr ba don yaso ba har ya samu ta haqura. A tare suka fito shida Rynt wacce har takai hannu zata bud'e murfin mota ta shiga ya daka mata tsawa yace"bana son raini tare mukazo ne! Kallon sa kawai Rynt tayi snn ta juyawarta ta kama hnyr fita riqe da er ledar ta da inna ta bata mai d'auke da kular d'an wanke a ciki. Tana fitowa gate d'in gidan sae mota ta gani a gabanta ta faka, snn aka zuge glass d'in motar a hnkli qoqarin kaucewa take sae taji muryar munir yana cewa"Rynt ina yini"kallon sa tayi sae kuma tayi saurin sadda kanta qasa tace "yaya munir barka da wuni"yace"lfy lau yasu inna da mohd tace"suna lafiya" Dukkan su sukayi shiru can munir yace" Rynt sae kuma naji.... yayi shiru sbd hawayenda suka cika mai ido, Rynt ma hkn ce ta kasance a gurinta,kmr daga sama taji muryar mohd yana cewa"ke je shiga mota gani nn zuwa. Ba musu ta wuce sbd kar kukan da take ji ya qwace mata mohd kuwa ba yabo ba fallasa ya ba munir hannu suka gaisa har ma yana tmbyrsa mutanen gida. Sai da suka gama gaisawa snn munir yaja motarsa shi ma mohd yaje ya shiga tasa motar, Da shigar sa ya kalli Rynt wacce tayi saurin sa hannu tana share hawayenta,kauda kansa yayi had'e da tsaki snn yace"da kina sonsa meyasa baki aure sa ba sae ni kika cutar"komai dae Rynt bata ce mai ba sae kauda kanta tayi gefe tana kallon titi. Da dare Rynt ce ta gama sllr isha'i tayi zaune shiru tana tuna irin wnn lokaci ne byn sllr isha'i mutanen qauyen su suka d'auki gawar mahaifinta izuwa maqabarta har tabi su tana ta kuka har sae da matan qauyen suka rirriqe ta......shigowar mohd ne ya katse ta ta kalle shi sau d'aya ta kauda kai tare da kai hannu ta share hawayen fuskarta. Yazo ya miqa mata wata babbar leda dake hannunshi yace"kar6i"ta kai hannu ta kar6a ba tare da ta ko kalle shi ba"yace"fito da duk abubuwan da ke cikin ledar" Sae da ta qara share hawayenta snn tayi komai yanda yace. School bag ce baqa mai kyau wankan gefe da littafan makaranta da biros da duk wani abu dai na aikin aji sae takalman mktrnta baqaqe da farar socks har da sabon niqabi yace" ki gwada takalman idan sun miki shikenan idan kuma basuyi ba kibawa mami ta maida min" Still sae da ta sake share qwallah snn ta gyad'a masa kai, shi kuma ya fita ba tare da ya damu da ganin kukan da take ba. Koda ta gwada takalmin dai dai qafar ta takai ta ajiye komai a cikin wardrobe d'inta sae ga mami ta shigo d'akin itama da nata kayan makarntar sae murna take itama za'a sata boko. Washe gari da safe mohd ya shigo d'akin yace da Rynt ya kyn komai yayi?tace"eh amma uniform sun min yawa, yace"u are very stupid! tun yaushe uniform d'in suke hannun ki baki tashi gaya min ba sae yau, wae ke bagidajiya ko, nifa ba haka bane ban duba kayan bane sae yau, oya je gwada kayan kixo in gani,tace"kawai ni a rage min ba sae na gwada ba"yace"ai sae kiyi ta zama dasu hkn nn tunda baza ki iya gwadawa ba, ya fad'i haka ne tare da juyawa zai bar d'akin tayi saurin cewa "dawo zan gwada,nn yaje kan sofa ya zauna ita kuma ta nufi toilet ta sako kayan ta fito tana d'an kame kame, qyar Man ke kallonta don bai ga abin kame kame a jikin ta ba, kawai dai ya fhmci yrnya ce sosai har dai da ta sanya uniform amma duk da haka dai baza tayi J.s.s ba SS one yake da burin sata in yaso ya kira mai lesson ya qara fhmtar da ita a gida. Yace"je cire kayan ki kawo taje ta cire ta kawo mai Bai kar6i kayan ba sae tsaki ya mata snn yace"to haka kike nufin zan fita da kayan ba leda" Kai tsaye taje ta saka kayan a leda ta kawo mai ya kar6a ya fita. Ajiyar zuciya ta sauke sbd ganin masifa irin tashi koba komai dai zata bishi a hnkli don ganin ta samu tayi bokon nn tukun. Sae dare ya maida mata kayan yace taje ta koma gwadawa ya gani idan sunyi,ta nufi toilet taje ta sako ta fito,abin mamaki idon sa ya kasa d'aukewa akan albarkatattun qirjinta da suka ciko rgr sae rgr ta mata mugun kyau,har dai da ta kasance farar riga ce mai dogon hannu da kuma corler ,saurin kauda idon sa yayi ya maida duban sa ga baby face d'inta yana mamakin jiya da ta saka kayan bai ma ga qirji a tare da ita ba ko don tufafin sun mata yawa sosai ne , nn dai ya basar yace"oya je cire rgr ki kawo min"taje bathroom ta cire uniform d'in ta kawo mai ,riga kawai ya kar6a ya bar wando a hannunta,tana tsaye ya bud'e buttons d'in rgr ya birkice ta,yaga da aka rage rgr ba'a yanke ta ba,hkn yayi masa dad'i don walwale d'inkin yake so zai yi ya maida ta er gidan jiya. Ya d'ago ya kalli Rynt tare da fad'in"bani reza"tace"me kuma zakayi?yace"har kya tambaya ke baki ga yanda rgr ta miki bane"tace"nifa dai dai tamin kuma haka nake son abuta"yace"kina da hknli ya zaki je da wnn riga a makaranta"tace"to ai da hijabi akai...koda hijabi akai idan aka yi rashin sa'a iska mai qarfi ya kad'a hijabin yazo ya kwashe malaman mkrntr suka ga yanda rgr ta miki kice me!shaye da toka tace"me kuma ya kawo wnn tunanin"tsaki kawai yaja tare da jefar da rgr ya fita daga d'akin. Ta bishi da ido tare da ta6e baki snn taje ta d'auki rgr ta linke kayan ta saka a wardrobe. Washe gari ne Monday tasha fad'a sosai a gun man kafin take gama shiri sbd tayi lettin tashi. Sunyi kyau sosai ita da mami dmn uniform d'in sun kar6e su. White hijab ,white head tight ,farar riga da kuma blue d'in wando, amma ita mami akan fara rgr ta akwai handlees jacket snn hijab d'in qarami ne sosai don da kad'an ya wuce wuya,na Rynh kuwa ya kai mata a cinya wanda tsaf ya rufe farar rgr da ke ciki. Duk makaranta d'aya za'a kaisu sbd makarantar tun daga kan nursery up to secondary school ake yi a ciki kuma mkrntr intanational ce ba laifi. Malika ce can sama a balcony tana shan iskar safiyar rnr ,sae dariya take hango Rynt da tayi wae ace zago zago da ita sae yanzun zata fara secondary school ko ya en j.s.s one d'in zasu kalleta ne oho,nn ta koma kwashewa da wata dry. 6angaren su Rynt kuwa man ne ya fito gidan sauri sauri wanda duk fad'an da Rynt tasha kan lettin da tayi sae gashi ta riga shi kammala komai ita da har mami sae da ta shirya ma. Yana isowa gurin ya kalli Rynt yace"bangane ba haka kike nufin zaki tafi fuskar ki a sake sae kace mai tallar fuska"tace"kmr ya bangane ba? Yace"bana son raini ina niqab d'inda kika gani a tare da kayan ne"tace"niqab a boko kuma ba sae lokacin islamiyya ko zan saka ba"ya watsa mata mugun kallo snn yace"da Allah malama ciro ki saka bana son raini! Rai 6ace ta bud'e jakarta ta shiga fito da littafan ta long books da suka nemi cika mata hannu bata kuma kai ga niqab d'in ba. Mohd yace"kar ki 6ata mana lokaci malama a ina niqab d'in yake? Tace" yana a cikin jakar"nn yasa hannu ya ciro niqab d'in,inda kai tsaye ya d'oro goshinta a qirjinsa yana d'aura mata niqab d'in sbd baya jin zai iya jiranta har ta mayarda littafan da ke hannun ta. Niqab d'in sae ya mata kyau sosai sbd yanda yalwatacciyar girarta ta fito tmkr ansa gazal had'e da manyan idanuwanta farare da kuma rabin karan hancinta ba kmr nata na islamiya ba da ba'a ganin komai na fuskarta. Mohd kuwa kallon wuyanta yake ta jikin hijabinta da yaga alamar bata kwantar da kwalar rgr ta ba. Guntun tsaki yayi had'e da zira hannun sa cikin hijabinta yana gyara mata kwalar rigar. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:19PM, 1/25/2017] Ummi Ya: [ 1/24/2017] 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 🔮🔮🔮 *page* *34* Saurin ja baya Rynt tayi shaye da toka tace"meye haka wae? Mohd ya dalla mata harara yace"bana son raini fa daga kawai kin samu na taimaka miki,da haka zakije collar riga a tsaye kina nuna musu asalin ke bagidajiya ce" Kallon sa tayi rai 6ace wacce ko niqabin da ya d'aura mata wani irin haushi ya bata har niyyar tayi ma ta ture shi sae kuma ta tuna mami na gurin. Yace"da Allah shiga mota kinyi tsaye kina kallon uwa wani baqonki! Nan taje ta shiga motar zuciyar ta sae quna take. Malika kuwa tun lokacinda taga man zai d'aurawa Rynt niqab ta sami kanta da miqewa zumbur sae kawai taga abinda yafi hkn wato hannun sa da ya zira a cikin hijabin Rynt. A zafafe cikin masifa ta kama hnyr saukowa ,sae dae koda ta fito tuni motar su tabar gidan. Wani irin qololon baqin ciki ne ya tokare ta a wuya, tace"kut zai dawo ya same ni ne wlh" Nan tayi zaune a falo sae zaman jiran sa take wanda yayi 30 mnt kafin yake dawowa, yana shiga ta tari gaban shi riqe da qugu ,yace"ke lfyrki meye hk? cikin masifa tace "har ka tambaya wane irin abin kunya ne naga kana aikatawa a d'azun ,bayan ka d'aura mata niqab bai ishe ka ba shine ka wani xira haunnunka a cikin hijabinta tir!A fusace yace"ba a hijabinta na zira hannu na ba a cikin rgrta na zira, very stupid in ke uwar cikina ce da zaki wani tasa ni gaba kina tuhuma ta da wani banzan shirmen ki can. Nn ya buga uban tsaki ya ra6a ta gefenta zai wuce, tayi saurin shan gaban shi ya dalla mata muguwar harara, da kanta tayi saurin bashi hnya ya wuce ta bishi da ido har sae da ya shige 6angaren shi snn tace"cabd'i lallai sae na tashi tsaye akan wnn er iskar yrnya,kai kuma dani kake zancen wlh zamu had'u a d'aki ne ai!snn ta tafi fuuu!zuwa d'akinta. Rynt kuwa gurin assembly students sae tsegumin ta suke ganin ta sanye da niqab kowa sae fad'in albarkacin bakinsa yake masamman da suka shiga class daga mai fad'in"ita wnn fa daga ina muka had'u da ita, sae me cewa qara'i sa niqab a secondary school ban ta6a gani ba, wata tace"hm koda kud'i wlh ba abinda zai sa na laqa wnn abun a fuska ta, wata tace inaga fa mtr aure ce don bazata sa niqab hk kawai ba, tace"wace mtr auren er qarama hk da ita kuma a ina kika ta6a ganin mtr aure a secondary school ai ko aure aka mata bata qare secondary school ba to sae dai kawai azo a zana mata waec n neco ,kawai dai inaga ma wani ciwo take d'auke dashi daya lalata mata duk rabin fuska shine akayi dabara da hkn. Duk zancen nn Rynt na jin su sae duk haushin man ya turniqeta don ganin take duk shine yaja mata wnn srtn gashi ta tsani irin haka,ai kuwa kai tsaye tasa hannu ta cire niqab d'in,masu gulmar ta suka ce"lah ashe yrnyr lafiyarta qalau ra'ayi ne kawai,yayinda wata ta kusa da seat d'in Rynt ta matso a hnkli tace da Rynt"sister meyasa kika cire niqabin nn kinyi kyau wlh bare gashi klr wandon uniform kuma yadin sa mai laushi da santsi baki ga yanda yayi kyau akan hijabin ki fari ba wlh da kin mayar zaifi ,tayi magana ne yayinda ta kar6i niqabin a hannun Rynt tana dubawa sbd ita dgske take yayi kyau,tace"ki myr kinji sister"Rynt tayi d'an guntun murmushi tace"ai zan mayar"ta fad'i hk ne kawai don ta huta da srtn yrnyr. Yrnyr tace"ok" Daga nn sukayi shiru sae ga wani uncle ya shigo riqe da register a hannun shi duk suka tashi tsaye suka gaida shi sae da ya amsa snn ya basu ixinin zama shima yaje ya zauna ya fara kiran sunayen su d'ayan bayan d'aya har ya kawo gun sunan Rynt da ya ji sunan ya soma masa wuyar fad'a sbd ba bahaushe bane shiyasa wasu abubuwa ke masa wuyar fad'a,wanda a lokacin da Rynt ta amsa sae da ya kalle ta dan ganin mai sunan. Sae five aka tada su sbd makarntar had'e take da islamiyya. Suna a tsaye ita da mami suna jiran tahowar man,nn Rynt ta ciro niqabinta ta d'aura sbd gudun masifar man, d'aura niqabin keda wuya sae ga motar man ta kunno kai. Da kanshi ya fito motar mami taje aguje ta rungume masa qafafu ,d'aukar ta yayi tare da kallon Rynt ta gaida shi ya amsa snn suka je cikin mota. Kan hanya mami ta kalli man da ke gefen hagunta yana driven sbd a gaban mota take zaune Rynt kuwa na baya. Tace yaya"Allah mkrntr nn da dad'i wata anti ta shigo ajinmu sae waqa take mana muna ta rawa kuma kasan me yaya? yace sae kin fad'a,tace"duk uncle d'inda da ya shigo ko aunty da waqa muke gaida shi na maka kaji,yace"yimin inji" Tace"kaga anti na shigowa zamu tashi tsaye ne "nn ta tashi tsaye snn tace"sae mu fara da cewa. _"Good morning aunty!we are very happy to see u!God bless u as u come today! Paa! pa papapa paaa!_ Muna tafawa itama tana tafawa snn sae tace "how are u? Muce we are fine aunty . Man yayi murmushi yace"to shikenan zauna ki huta"turo baki tayi tace "yaya ban fa gama baka labari ba"sae da ya shafi fuskarta snn yace"to mami zauna sae kici gaba da gaya min" Bata zaunan ba sae cewa tayi"bayan mun zauna sae ta mana waqa mai dad'i muna ta rawa abin mu kuma itama tana kama mana,na maka kaji ita ma?eh inaji, ta fara da _"1,2 bought my shoes! 3,4 knock at d door!5,6 pick up sticks! 7,8 let them straight !9,10 a big fat hen!11,12 shoot ur gun! du! du!dudu! duu! I said shoot ur gun du!du!dudu! duuu!"_ Dariya ce ta qwacewa Rynt wacce tun d'azun take fmn danne ta amma ta kasa. Sbd yanda mami ke rawar waqar abin dariya ne sosai. Ta jikin mirror man ya hango Rynt dake fmn dariya sbd fuskarta ba niqab da shigar ta motar ta cire ta kad'a jaka. Rynt ta tsagaita da dariyar ta yayinda mami ke cewa"Anti ai kuma yau kunyi ta rawa da waqa ko? Tace"Aa mami ai mu ba yara bane kmr ku"to Anti ai auntyn mu ma babbace amma takeyin rawa"eh ita malamar yara ce shiyasa, to anti meyasa kullum sae naga anti amarya nasa kid'a tana ta rawa bayan ita ba malamar yara bace? Nn Rynt tayi rashin sa'ar had'a ido da man ta jikin mirror sae kawai ta kauda idonta tayi kmr ma bata ganshi ba tace da mami"wae mami ba islamiyya aka tashi ba yanzun nn amma sae zancen boko kike mana da tun qarfe biyu aka wuce gun" tace"yauwa anti a lokacin islamiyya ko, wani malami yace yana sona qanwa tunda na iya alfun ba'un har qarshe kuma ba kuskure ko d'aya ,nace masa ai antina ce kullum take koya min a gida har ma nace ko shi idan yana so yazo zaki koya masa,ko anti zaki koya mai in yazo ko?Rynt tace"uhm mami ai shi malami ne yafi ni iyawa sae dai ma ya koya min, to anti ai da na gaya mai a mkrntar kike yace yana so zai ganki sbd yaji dad'in yanda aka bani kulawa har ma nafi en ajinmu iya karatun qur'ani. Mohd yace"mami ba kya gajiya da surutu ne wae nikam, a ajiye zancen nn haka kinji, kuma ki daina fad'ar abinda ba'a tambaye ki ba kinji,tace" to yaya zan tambayeka gobe idan zaka kawo mu school zaka saya min chocolate kan hanya sbd wanda ka saya min a kwanaki ya qare gashi yau da mukaje breakfast ina ta gani agun en ajin mu suna ci har da biscuit amma ni banda" Yace"ai mami na siyo miki komai suna but na manta dasu ne. Yauwa yaya na gode yanzu in muka isa gida sae a ftr ko? Yace "eh"nn ta kama waqar ta. _pawpaw is a kind of fruit,sweet like sugar yellow like fanta every body like pawpaw ,pawpaw!_ _A lion !a lion!a lion has a tail he has a big head and a very small waist._ Haka tayi ta en waqoqinta sbd dama ta iya duk wasu waqoqi da take ji a bakin en gidan su. Man dai da Rynt ba mai magana a cikin har suka isa gida. Tun daga rnr man bai qara kaisu school ba driver ke kaisu yana d'aukosu. Rynt kud'in break fast yake bata mami kuwa kuku ke had'a mata breakfast asa a lunch box. Haka kuma tun daga rnr Rynt bata qara yadda taje da niqab a school ba sae dai idan zasu je takan sa da sun isa mkrnt se ta cire idan kuma zasu koma gida ta saka. Yanzu har sunyi kusan sati biyu da fara zuwa makaranta amma har yanzu mohd bai nemowa Rynt mai lesson ba. Rnr wata juma'a da qarfe 12:05pm man ne tsaye a parking lot ya bud'e gambun mota zai shiga sae ga su Rynt an dawo dasu daga school. Ko tsayuwa motar su bata gama yi ba Rynt ta bud'e gambu ta fito mota ta tafi aguje cikin kuka ta shiga gidan. Man dake qoqarin shiga mota sae fasawa yayi ya rufe gambun mota snn yabi Rynt cikin gida. Ya same ta zaune kan bed ta had'e kai da guiwa tana ta kukanta. Zama yayi kan bed d'in had'e da kai hannu ya riqo hannun ta da yaga duk shatar bulala ne akai, yace"waye ya dake ki?warce hannun tayi tare da d'ago fuskarta nn hawaye suka silalo a hnkli kan kumatun ta ,ta share hawayen wasu suka koma zubowa tace"wani malami ne ya daken"me kika masa?wae cewa yayi nayi kuskuren fad'ar wata kalma a cikin wani littafin turanci da yake karanta mana tun satin da ya gabata shine yau yace kowa sae ya karanta d'aya byn d'aya,to shine da ina karantawa na kawo gun wata kalma ya dakatar dani yace na sake maimaitawa na maimaita masa ,sae kawai ya shiga min fad'a wae irin mu ne basa maida hnkli a aji gashi har nakai ss one amma bana bawa kowace kalma haqqinta,sae yace kuma bazan zauna ba har sae na iya kalmar. nn yace duk ya fad'a na fad'a mukayi hkn har sau uku,amm yace bnyi dai dai ba nn kawai ya kira wata yace ta fad'i kalmar yaji ,tana fad'a yace a tafa mata ni kuma ya zane ni ya kuma sa aka min kuwa. ta qarashe mgnr cikin kuka sosai snn ta d'ora da cewa "kuma wlh dai dai nake jin ina fad'a amma shi sae yace banyi dai dai ba" Man da tun lokacin da Rynt ta fara zancenta ya kafe ta da ido, ya sauke numfashi a hnkli snn yace"fad'i kalmar naji" tace"retyfe" yace"retype"tace"eh"yace"kinyin kuskuren fad'a mana,dmn kinsa harafin da bashi ne a cikin kalmar ba, ma'ana p ake son sautin ta ya fito ba F ba"tace nifa bangane ba, yace"ok saurareni kiga kuma ki kalli bakina yanda iskan kalmar zai fito a bakina"ta gyad'a mai kai tare da tsure bakin shi da kallo"yace"retype,retype,retype har sau uku snn yace kinji yanda nake fad'a ba kmr naki ba? cikin murya kuka tace"gsky ni banji wani banbanci ba"yace"bani aron yatsan ki d'aya"shaye da toka ta kalle shi don ita ta tsani haraka da yace zai ta6a ta, sae dai kuma tana son ta gano meye kuskuren ta a cikin fad'ar kalmar. Haka ta daure ta miqa masa d'ayan yatsan ta ,ya riqo yatsan a hnkli yakai saitin la66an sa yace"retyfe" kmr yanda take fad'a kenan yace"to ya kika ji iskan bakina ya sauka a yatsan ki da qarfi ko a hnkli? Tace a hnkli naji, yace "yauwa yanda kike fad'a kenan amma yanda ainihin ftr sautin kalmar yake shine "retype"to ya kika ji wnn iskan nata ya sauka?a hnkli ko da qarfi? tace"da qarfi"ya sakar mata yatsa snn yace"to haka nake son ki fad'i kalmar sau uku inji tace"retyfe,retyf.....ba haka ba, look kalli la66a na da kyau kiga yanda nake had'a la66ana gurin fad'ar kalmar musamman gurin p kinji ko,a sanyaye tace "to"snn ta tsure la66ansa da kallo ya fad'i kalmar kusan sau biyar snn yace"oya fad'i naki inji"sae da ta rufe ido tana mai tuno yanda la66ansa ke had'uwa da kuma yanda yake ftr da p, ta fara da cewa"Retype ,retype,retype"har sau uku snn ta bud'e idanuwanta kmr zatayi kuka don har sun d'an ciko tace"hkne kokuwa har yanzu ban fad'a dai dai ba? A hnkli ya lumshe ido ya kuma ware su a kanta snn yace"kinyi dai dai. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:19PM, 1/25/2017] Ummi Ya: [ 1/25/2017] 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 🔮🔮🔮 *page* *35* Ya tashi zai fita ,har ma yakai bakin qofa ya juya gun Rynt yace "mami fa? Tace"tana gida muka ajiye ta sbd tace tana son tabi mama anguwa ne" Sae a snn ya tuna da safe kafin su fita ya ba mami waya tayi waya da ummarta. Yace"ok ki shirya anjima da qarfe 4 mai lesson d'inki zai fara zowa" Dad'i taji sosai don har godiya sae da ta masa snn ya fita. Yana fitowa ya had'u da malika zaune a falo,kafin ya qarasa gareta ta wani sha toka yaje ya zauna kusa da ita tare da rungumo kafad'ar ta yana mai kallon fuskar ta yace"lfy me akayi kuma? Tace"nifa bangane ba don naga kmr ka fara kula yrnyr nn " yace"kin manta yanda mukayi dake ne?ban manta ba amma ai.... um um kin fasan bana son qananun maganganu da zasu riqa zowa suna kawo sa6ani a stakanin mu,tace"to shikenan ya alqawarina da kamin, yana nn amma ai ce maki nayi ki bari idan an dawo daga masallaci ko,eh to na shirya kenan kafin ka dawo? Eh. Ya tashi ya fita ita kuma ta koma d'akinta. Bayan ya dawo daga masallaci ne suka fita anguwa shida malika. Gidan wata qawarta ce ya kaita. Bayan sun gaisa har qawar ta kawo mata abin sha da na motsa baki tace"oya gareki"malika tace"hm tukuna dae nifa kinsan na gaya miki ina cikin damuwa"qawar tace "damuwar me kuma gudar mtr man dake"hm fa'iza kenan man d'in da ke qoqarin juya akalar sa wni gurin" kmr ya ban gane ba?ina nufin ya fara kula wnn abar mana da ubansa ya aura masa......mtsw ita wnn abar ce har zata saki a damuwa wlh da nice ai da tuni nayi waje da ita,,ta yaya bayan dole sae ya saketa ne ko zata bar gidan..... Kaji wata tsiyar sae kace ba mace bace ke kai inama nice da wlh tun rnr da aka kawo ta gidan bazata kwana ba ,fa'iza kin manta sae da akayi sati d'aya nsn cewa tana gidan, to byn nn me kika iya yi gashi har yanzu kin kasa aiwatar da komai. Dafa na mai mgnr ta sae ya cemin baya son jin zancen ta kwanaki har dukana fa ya tashi yi akn hkn....kayya! me ya shafe ki da yi mishi zancenta kawai ki guma mata uban sharrin da zai rubuta mata saki uku zama d'aya!hm aike na fara gwada hkn ashe er iskar yrnya baki ne da ita, tamin zagi mai ciwo ta alaqanta Abbana da sharrin da na mata,nn ta gaya mata labarin yanda sukayi snn tace"wlh har yau ina da burin cin qaniyar ta don ba barin ta zanyi ba" kai!! Kutumar uba! Cewar qawarta wacce duk ta cika da jin haushin malika. Tace"malika gaya min abinda man yafi so a rayuwar sa"tace"ko meyasa?kedai gaya min nace! malika ta ta6e baki snñ tace"hm to shifa wae ba abinda yafi so irin yaga na sami ciki ni kuma wlh bazan bari ba don ban shiryi haifuwa yanzu ba" Tace"common bari kawai ki sami ciki"tace"cabd'i kan me!tace "bani kunnen ki kiji, nn ta rad'a mata magana malika ta washe baki tace"Allah? Qwr tace"wlh kuwa ba boka ba malam kuma buqatar ki ta biya. Malika tace"wlh kin bani gud idea don wlh yanda yake son in samu ciki ko, duk na mata sharrin nn da kika gaya min to wlh ido rufe zai saketa don ubanta har wae boko ya sakata.... Ya akayi kika barshi... Wa kin fa san ko waye man ba irin mazan da ake tanqwasawa bane wlh duk yanda naso yimai rashin mutunci sae ya taka min birki kuma wlh idan yana min fad'a zaki rantse auren qiyayya mukayi nida shi, sbd shi komai baya sakawa cikin wani ,don lokacin soyayya kam zamu zubata nida shine kmr zamu kashe juna amma da nayi mai laifi to fa zai ajiye so gefe har sae yayi min tas snn ko zamu dawo dai dai daga baya. Qwr tace"lallai man d'in nn naki da wuyar sha'ani yake ni mijina ya ma isa ya tunkare ni yace zai min fad'a hm wa albarkacin gawa ta zagi mai mata wanka!kin ganni nn wlh tun ina amarya bana ko kauda kara duk aikin da nazo yi sae kiga ya kar6e yanayi wae shi baya so na wahala ae kuwa nace da kyau aini dama ta sameni don maida shi nayi tmkr shine mtr nice mijin ,Allan dgske fa'iza? Wlh kuwa ba taqamar sa baya son na wahala ba ai kuwa wahalar zata tabbata akanshi,hm cabd'i ni na isa nace zan juya man ai sae dai ko aikin boka, don kinga ko yanzu cewa nayi ya jirani a waje ba wani jimawa zanyi ba in na fito sae yakai ni gida,yace"shifa baya d'aukar irin wnn raini tunda tun farko nn kad'ai nace masa zan zo don haka zancen gida sae kuma wani lokaci, sae da na d'an had'a masa da kukan shagwa6a snn fa yace to zai je ya dawo ya kaini ,au da sauqi kenan tunda idan kinyi shagwa6a yana duba miki, hm ai mayen son shaw6a ne in gaya miki yafi son ya ganni narke kan jikin shi ina ta zuba mai shagwa6a sae kiga yana ta min abubuwa a jiki sae wani tatta6a ni yake yana wani romancing d'ina,ni kuma ba abinda nafi so irin aje ga babbar haraka amma shi bai cika son wnn abun ba yafi so muyi ta wasa ko za'a kwana ma ransa bazai 6aci ba. Qawar tayi dariya tace"lallai gayen nn naki sae shi,hm basshi ai wani lokacin har fad'a mukeyi dashi wae na fiye buqata yace idan har wani abu nake sha gwanda ma na daina bcs too much sex ba'a cika marmarin juna d'in nn kmr idan aka jima ba'ayi ba. In gaya miki nidai jinsa kawai nake don wani lokacin har zuba mai desire tablet nayi a coffee ai kuwa rnr kaf dare muka kashe muna abu d'aya sae safe nayi ta mai sharri nace su oga ya akayi jiya ka tsunduma a haraka sosai kaida naga baka son haka ,da yake gayen nawa baya son raini sae ya wani tsare gida yace"rnr jiya ta daban ce shiyasa",kuma kin san me ashe ya gano ni fa don washe gari dana zuba masa maganin a coffee wlh cikin dabara ya d'ura min shi tas na shanye shi bai sha ba,kuma yamin qeta ya rufe ni a d'aki ya tafiyar shi,hm wlh kasa bacci nayi rnr har safe. Qawar tayi dariya snn tace"wlh ki rage yawan buqata don ina gaya miki yana sa ki fita a ransa tace"hm wlh ni kuwa ba abinda nafi so irin naji inada buqata shiyasa bana ta6a yarda desire tablet ya yanke min,kema ki koya don zaki fi jin dad'in rayuwarki haka. Hm wata jaraba ce kuma wnn. Fa'iza tace"hm laila, ni mijina ma da sae ya min kuka nake barin shi....nn wyr malika tayi qara ta kalli fa'iza tace"kinga tafiyata my man ya dawo , tace"to yayi sae nazo a gaida shi tace"to snn ta d'aga wyr ta fita. Rynt kuwa koda qarfe hud'u tayi ta gama shirin ta tsaf sae jiran mae lesson take amma shiru har aka qara minti goma sae ga man ya shigo d'akin yace da Rynt"zo ga mai lesson d'in naki yazo"ta taso zata fita ya kalle ta shaye da toka yace"bana son raini fuskar ki zai karantar ko ke! da zaki wani je masa fuska sake ba niqabi" Tace"wae nikam meyasa kake son takurani ne kace komai sae nasa niqab" Yace"kika dae takura kanki ai na gaya miki tunda kikayi gigin amincewa aurena baxa ki ta6a jin dad'i ba,rayuwarki da mami ne yasa nake d'an sauqaqa miki ba wae don wani abu ba! Don hk ki tabbatar kin saka niqab kafin ki tafi idan ba hk ba kin haramta da lesson d'in gabad'aya! Nn ya tafi ya varta tsaye ta ta6e baki tace"auren naka in banda qaddara me ma zai sa na amince ko yanzu cikar burina kad'ai nake jira na fecewa aurenka" Taje ta ciro niqab ta saka snn ta fita. Man na zaune ake mata lesson d'in hkn yasa yaga yanda Rynt keda saurin fahimta duk da cewa hnklin sa ba duka yana kansu ba sbd wani aiki da yake a laptop. Sae da ana kusa fara kirayen kirayen sllr magrib mai lesson d'in ya tafi. Ita kuma ta tashi zata tafi kenan man ya tsaida ta yace"gaya min kalmar da na koyadda ke a d'azun "sae da ta kauda kanta gefe snn tace"retype"ya d'an d'ago ya kalleta snn yace jeki. Bayan sati d'aya da faruwar haka fhmtar Rynt sae qaruwa take akan lesson d'inda ake mata don yanzu ta fara fhmtr wasu kalmomi na turanci da ake fassara mata su zuwa hausa,hkn kuma akan nuna mata yanda ake ftr da sautin kowane harafi da kuma sauran abubuwa da dama. Mohd kuwa duk za'ayi mata lesson sae yazo yayi zaune a falo sae ya fake da wani aiki ne yake kan laptop hkn bai hana Rynt ta kasa sakewa ba a gurin lesson d'in sbd sosai take son ta fahimci komai ko don yanda a class take jin ana fad'in wasu kalmomi da dama na turanci da bata san su ba. Gefen islamiyya kam Alhmdlh bata da wata matsala gurin, kuma still tana ci gaba da maida hankalinta sosai akai. Ko yanzu ma lesson ake mata man na zaune yana aiki da laptop d'inshi . Yatsun sa na kan laptop amma sae kallon Rynt yake sbd yanda ta bada dukkanin hnklinta akan lesson d'inda ake mata da kuma wasu tambayoyi da yaji an mata ta bada amsa kai tsaye. Can Rynt taji a jikinta ana kallonta hkn yasa ta d'ago sae kawai ta sami idanuwanta a cikin nashi still bai daina kallonta ba sae itace ta maida hnklinta ga lesson yayinda kyawawan yatsun ta ke riqe da marker ta fara rubutu akan whiteboard d'inda ke gabanta zata had'a sentence akan wata kalma da lesson teacher d'in ya bata ta rubutu sentence akai dmn yaga idan ta fahmci ainihin inda ake saka kalmar a cikin magana,kmr yanda ya mata bayani. Shiyasa man ya kasa d'auke idonsa dmn yaga shin zata iya. Tsaf kuwa Rynt ta had'a sentence ba wani gargada ko shirme a ciki, qoqarinta man ya gani ba don komai ba sae don sanin ba wani gud foundation ta samu ba amma gashi tayi trying much better akan lesson d'inda ake mata da ba'a wani jima da farashi ba. Numfashi ya ftr a hnkli had'e da maida duban shi gun laptop yayinda su kuma suka ci gaba da lesson d'insu. Washe gari da qarfe kusan uku malika ce zaune a falo ita kad'ai tana jujjuya wasu ruwan gora dake hannunta nn wayarta tayi qara ta d'aga wyr tare da tashi ta nufi fridge d'in falon ta saka gorar a ciki snn ta nufi d'aki ta d'auko mayafinta ta fita. Ba jimawa sae ga Rynt ta fito falon riqe da magani a hannunta zata sha sbd kanta da taji yana d'an mata ciwo gashi to 4 mai lesson d'inta zai zo. Tana bud'e frigde d'in sae ga man ya shigo gidan ya nufi fridge d'in ya buga tsaki ganin gorar ruwa qwara d'aya wanda tun jiya ya kamata ace ya siyo ruwa a gidan amma sae gashi yau ya fita ya manta. Ya kalli Rynt tare da fad'in "ke kin gyara min d'akina kuwa? Tace" bana jin dad'i ne amma yanzu zan tafi idan nasha magani " Yace"kin fara ko? tace"nifa ba hk bane kuma kasan bana iya gyara d'akin naka ba kowa a ciki, mami ce ke tsaya min kuma bacci take tun d'azu amma idan zaka tsaya min zan gyara maka ynz" Bai ce mata komai ba sae gorar ruwa ya jawo ya tsiyaya mata ruwan a cup ya bata snn shima ya tsiyaya ma kansa yasha. Malika na cikin mota ita da qawarta fa'iza tana driven zasu tafi kasuwa sae fira suke malika ta katse firar da cewa"oh my goodness!fa'iza na manta na saka gorar ruwana a fridge d'in falo a maimakon nakai d'akina"fa'iza tace "to meye matsalar ko gidan naku tsiyar ruwa ake yi ne" Cikin ba'a fa'iza ta fad'i mgnr ,malika tayi murmushi tace"ba haka bane desire tablet ne a cikin su kuma mai qarfin ne da sae dare nake shan shi idan zamu kwanta nida my man. Fa'iza tace"to ai sae ki bari idan kin koma kya cire" Malika tace" Eh dama ai" Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [10:42PM, 1/27/2017] Billy giro😊: [ 1/27/2017] 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 🔮🔮🔮 *page* *36* 6angaren su Rynt kuwa man yana gama shan ruwa ya tafi d'akin shi riqe da sauran ruwan da ke cikin gora,sae a snn ne Rynt tasha magani tabi bayan shi dmn gyara mishi d'aki. Ta same shi yana qarasa shanye ruwan da ke cikin gora, sae da ya shanye ruwan tas snn ya jefa gorar a dustbin ya zauna kan sofa tare da jingina bayan shi ya kuma lumshe ido kmr wanda zaiyi bacci. Ita kuwa taje ta fara gyara mishi bed yayinda man ya fara jin wani yanayi a jikin shi na daban yadai basar ya tashi zai je bayi Rynt tace"nifa kar ka tafi koina kabari har na gama gyara ma d'aki tukun don ni tsoro nkeji,kmr bada shi take zancen ba ya shige abinshi ya watsa ruwa sauri sauri ya fito sanye da white bathrobe yazo yayi tsaya a bakin qofa yana kallon Rynt yace"ke ajiye gyran gadon kixo ki wanke min bathroom tukun. Rai 6ace ta ajiye gyaran gadon taje da niyyar shiga bathroom d'in amma man bai bata hanya ba sae kallonta yake sbd wata irin mahaukaciyar sha'awa da yaji tana fizgar shi. Rynt kuwa ganin baya da niyyar bata hanya sae tsaki ta buga ta juya zatayi tafiyarta ya fizgo hannunta da qarfi ta fad'o kan qirjin shi, tayi sauri zata fizge kanta ya qara matse ta sosai a qirjin shi,yana binta da wani irin kallo, tace"wae meye haka ne" yace "ni zaki ma tsaki"tace"to ai kaine kaqi ka ban hanya" Ya saketa tare da kashe wutar d'akin ya koma jawota ya rungume ,cike da tsoro tayi saurin kallon shi tace "meye haka kuma"yace"zan kar6i haqqina ne" Cikin mugun tsorata da jin zancen sa tace"haqqin ka kuma! Yace"eh ko zaki hanani kar6a ne? Bata bashi amsa ba sae fizge kanta tayi ta tafi aguje zata bar d'akin yayi hanazarin kamotà ya cicci6e ta yakaita kan bed ya jefar kmr wata kayan banza. Kafin tayi yunqurin tashi sai jinsa tayi kan jikinta ya mata rumfa tare da daddane mata hannuwa . Nan ta shiga qoqarin qwatar kanta tana fad'in"wae me kake nufi da haka ne,ni dan Allah ka sake ni natafi kar mai lesson yazo ya samu ban shirya ba" Bai kula ta ba sae hjbnta yake kiciniyar cirewa. Yayinda Rynt taji wata irin kasala da sabon yanayi sun fara saukar mata a jiki" Da har man ya iya nasarar cire mata hjb yakai hannu yana bin fuskarta da shafa har izuwa wuyanta ya kuma kwanto sosai a qirjinta zai had'e bakin su. Tayi saurin kauda bakin ta tare da fashe mishi da kuka tace"don Allah kayi haquri wlh nayi qanqanta da wnn abun "yace kinsan kinyi qanqanta amma kika amince da aurena"tace"nidai dan Allah kayi haquri kaje gun mtr......bakinsa kawai taji cikin nata ya kuma kai hannu cikin rgrta yana wasa da na fulaninta, tana ji har yayi nasarar rabata da komai na jikinta ya fara wata sabuwar wasa da jikin nata. A mamakinta sae taji ta kasa hanashi komai sae ma wani qara narke mai da take jin tanayi sbd sharrin desire tablet d'inda yayi galaba a kanta ,sae dai man ya fita tsunduma dmn tuni shi yayi nisa da barin hayyacin sa. wanda ba wani lalla6awa yake yunqurin zuwa hnyrda a hnkli ya kamata ace ya bita. Rynt kuwa duk da irin kamun da desire tablet ya mata sae da ta shiga kokawar hana faruwar hkn amma sam bata da wani qarfi. Ihu take tana kuka sbd jin zafin baqon al'amarin da ya shiga faruwa da ita, amma sam man bai saurara mata ba har sae da yaji ya samu kanshi yanda yake so. Snn ya wani tashi zumbur daga kan jikin Rynt da ke wani irin wahallalen kuka,da sauri yakai hannu ya murza idon sa wae ko zae samu mfrki yake,ya tuna tabbas ba mafrki bane sbd yanda komai ya shiga dawo mai tun daga farko. Sosai ya shiga mamakin kansa wae ace shine ya neme ta da knshi, wane irin abune ya same shi yau shikam. Jiki sanyaye ya jawo bathrobe d'insa ya saka had'e da kallon Rynt cike da tausayi ganin yanda ya mata liga liga,ya kauda idon sa gefe ya fara sauka kan gadon bai qarasa sauka ba sae qafafuwan sa da ya saukar tare da dafe kansa, ya d'auki lokaci mai tsawo a hk snn ya tashi ya bar gadon ya nufi bathroom yayi wanka ya fito. Ga mamakin sa bai sami Rynt ba ta fita d'akin. Zuwa yayi ya cire bedsheets din gadon yaje bathroom ya saka a washing machine ya fito. Yana fitowa ya samu wyrsa na ruri koda ya duba mae lesson d'in Rynt ne nn ya d'aga wyr . Bayan sun gama gaisawa mai lesson ke ce mishi tun d'axu yazo yayi ta danna door bell ba alamar akwai kowa a gidan,mohd yace"muna ciki ba muji bane amma kayi hqr ka tafi kawai sae gobe don yau bata jin dad'i ,nan ya mai Allah sauwaqa snn suka ajiye wyr. Ya nemo farar jallabiyar sa ya zira ya tafi masallaci yayi sallar la'asar ya dawo yayi zaune a nn falo yana mai kallon gefen d'akin Rynt wacce yasan ba lallai bane ta iya ta6ukawa kanta wani abu amma sam baya jin zai iya zuwa ya taimaka mata don bai san da wane irin klr raini zata zo mai dashi ba. Tashi yayi ya nufi fridge dmn ya samu yasha ruwan sanyi ko zai ji sauqin haushin kansa da yake ji. Sae da ya bud'e fridge d'in ya tuna ba ruwa hkn yasa ya ciro fresh milk ya tsiyaya a cup yasha snn ya ciro wyrsa a aljihu ya kira kuku. Suna gama waya dashi ya tafi d'aki ya d'auko kud'i ya fito dai dai kuku ya shigo gidan ya miqa mishi kud'in tare da list d'in abubuwan da zai siyo sbd wayr da sukayi akan zai siyo abubuwan da babu ne a gidan. Malika kuwa ba ita ta dawo gidan ba sae byn isha'i ta sami man zaune a falo yana kallon labaru sae dae hknlinsu kwata kwata baya gurin don har lokacin tunanin abinda ya faru shida Rynt yake wacce har yanzu bai sa ta a ido ba. Kan jikinsa malika taje ta kwanta tare da fad'in "waeh Allah my man yau nagaji da yawa har ma wani baccin wahala nakeji" Yace "aikin me kika yi ne?kasuwa mana my man,wace kasuwar ce tun d'axun baki dawo ba sae yanzu?gida na tafi my man umma ce bata jin dad'i kuma nayi ta kiran wyrka baka d'aga ba, shiru yayi don sae a lokcn ya tuna yaga miscalls d'inta har uku, yace "to ya jikin nata tace" jiki da sauqi" Tana gama fad'ar haka ta tashi tare da fad'in ni zan tafi na d'an watsa ruwa. Yace"ok"tace"ko zakayi ne mu tafi? Yace"Aa"ta kallesa da kyau dmn ta fhmci kmr yana cikin damuwa tace"my man meyake damunka ne? Kallon ta yayi yace"ba komai" Bata sake tmbyr sa ba ta nufi fridge ta bud'e. A maimakon taga gora d'aya sae tagansu da yawa da sauri ta shiga duba bakin kowace dmn ta bud'e tata gorar sha ne kawai batayi ba,sae kuwa tayi sa'ar samun gorar da aka bud'e ba'a sha ba,ta d'auki gorar zata wuce man yace"bani gorar ruwa d'aya a gurin ta d'auko ta bashi ya kar6a ya kai hannu zai bud'e gorar sae ya tuna d'azu ya bud'e wata gorar ruwa bai sha ba ya maida a fridge,nan dae kawai ya basar ya bud'e gorar ya tsiyaya ruwan a cup yasha . Malika kuwa tana bashi ruwan ta wuce zuwa d'aki riqe da ruwanda ta d'auka ko sune ruwanta. Mohd na gama shan ruwa sae ga mami tazo gurin shi tare da jawo hannun shi tace"yaya zo muje kaga Anti tun d'azu sae kuka take tayi kuma idan na tmbaye ta me take ma kuka bata min magana. Ba musu ya bita sukaje d'akin Rynt wacce ke zaune kan sallaya ta had'e kai da guiwa tana fmn kuka. Kuyi hqr da wnn snn kuma kuyi hqr da rashin samun shi kullum muna fama da mtslr nepa ne. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [10:15PM, 1/28/2017] Billy giro😊: [1/28/2017] 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 🔮🔮🔮 *page* *37* Mohd yaje ya durqusa gab da ita yana mata magana amma taqi ko d'ago kanta bare zancen bashi amsa sae ma sautin kukanta da yake qaruwa. Man yayi shiru yana tunanin kodai ya mata rauni ne. Yace"Ki min magana naji idan kin samu rauni ne na baki magani" Mami tace"yaya hln me ya sami anti da zata ji rauni? Yayi saurin kallonta don ya manta ma tana d'akin yace"ba abinda ya sameta kawai bata jin dad'i ne ,je downstairs ki d'auko mata ruwa a fridge tasha magani"tace"to" snn ta tafi da gudu. Shi kuma bai sake ce ma Rynt komai ba sae bedside drawer yaje ya bud'e ya ciro magunguna ya kawo gabanta ya ajiye. Dai dai mami ta kawo ruwan ya kar6a ya ajiye a gbn Rynt ya tashi tare da riqo hannun mami suka fita. Suna fita Rynt ta ture gorar ruwan har ma da magunguna ta fashe da kuka sosai, ta samu ta miqe tsaye da qyar wacce hjibinta duk yayi sharkaf da hawaye ga idanuwanta da suka kumbura sukayi jajir kan kuka. Bata damu da ta cire hijabin ba sbd baqin ciki da damuwar da take ciki kad'ai sun ishe ta. Taje kan bed tayi kwance tana ci gaba da kukan da ya fara saukar mata da zazza6i. 10:00pm Man ne kwance cikin shirin sa na bacci malika ta shigo d'akin taje gab dashi ta kwanta suna masu fuskantar juna ta shafo gefen fuskar shi snn takai hannu tana scrolling din wyrta tace "my man style d'in kwanciya na samar mana duba kaga, wata muguwar harara ya watsa mata yace"wae bana hanaki kallon abubuwan nn ba! ta 6ata fuska tace"nifa matsala ta dakai zafin zuciya wnn fa photo ne ba video ba,kuma wlh da gani style d'in zamu ji dad'in shi sosai don ina ganinsa sae duk na kasa samun natsuwata. Yace"wae ke ce maki akayi anayin aure ne wa abu d'aya,da kullum bakida wata magana sae ta kwanciya" yayi tsaki ya juya mata baya yana fad'in" wata in kuka take a rnr farkonta wae ke a taki rnr har ma kin fini zu6ud'i. Tace"me kace?yayi banza da ita, Ita kuma ta buga tsaki ta fita ta bar d'akin rai 6ace. Washe gari ta kasance rnr lahadi. Mami kad'ai aka kai islamiyya sbd zazza6in da ya rufe Rynt sosai wacce ba yanda man bai yi ba kan ta bari ya mata allura amma taqi da qarshe ma inna yaje ya d'auko ya tafo da ita. inna sae lallashin Rynt take ,Rynt tace"Bana son allura inna kuma don Allah kice ya tafiyar shi"inna tace "jikin ki yayi zafi sosai Rynh kiyi hqr ya maki allura kinji" Tace"Ni inna a bani magani kawai nasha" Inna tace"to kaji had'o mata magunguna tasha" Mohd yace"inna dole ne fa sae an mata allura snn ko zata d'ora da magani" Nn inna ta koma lallashin Rynt har ta yadda a mata allura amma a hannu . Man na had'a allura sae kallon Rynt yake wacce ta 6oye fuskarta a jikin inna sbd bata son ganin tsinin allura. Bayan ya mata allura ne inna ta kai hannu tana murza mata gurin. Snn tace"to sauko qasa kici abinci don nsn ko lafiyar ki qalau ba wani cin abinci kike ba bare babu lafiya,ga muhammadu ba kula ne dashi ba shidai cikin sa kawai ya sani. Komai dae mohd bai ce ba sae harhad'a kayan allura yake ya kai drawer ya ciro magunguna ya ajiye a cewar idan taci abinci sae tasha. Har ya kama hanya zai fita yayi saurin juyowa sbd Rynt da yaji tace"wash Allah inna bazan iya ba bari kawai naci abincina a nn kan gado"inna tace"yo Rynh ai ba kyau cin abinci kan gado" Tace "to inna a ajiye kawai har idan na tashi zanci"Aa ba'ayi hk ba zan dae baki kwanon abincin ki riqa a hannunki sae kici tunda dae ya zama lalura" Inna ta d'auko plate d'in abinci ta miqawa Rynt wacce garin kar6a ne idonta ya fad'a kan man rai 6ace tayi saurin kauda idonta shi kuma ya fita. Inna ta jima kafin take barin gidan wacce bata san ainihin abinda ke faruwa da Rynt ba ta d'auka ko ciwo ne kawai. Bayan sllr la'asar mai lesson d'in Rynt yazo. Bayan man ya gama gaisawa dashi ne ya nufi d'akin Rynt ya samu sae bacci take qudundune cikin blanket ya matsa gab da ita da niyyar ta6o jikinta yaji idan ya rage zafi sae kuma ya fasa sbd tuna cewa zai iya tasheta tunda ba wani nauyin bacci ne da ita ba, kuma alamu sun nuna mae bata jima da yin baccin ba sbd eyelashes d'inta da ya gani d'auke da sanyin hawaye. Juyawa yayi ya bar d'akin yana tunanin ina ma mami na nn da sae a mata lesson don dama yana da niyyar a had'a har da ita a riqa musu lesson amma ba'a lokaci d'aya ba tunda abubuwan ba d'aya bane idan dae an gama ma wnn sae ayima wnn. Haquri yaje yana ba mae lesson d'in sae ga malika ta fito , mai lesson yayi saurin kauda idon sa ya fita sbd kayan jikin malika ba na kirki bane. Man ya kalleta yace"kin manta kayanda ke jikin ki ne da zaki ganni da wani kuma ki fasa komawa"ta6e baki tayi tace"to yi hqr, but waye shi? Sai da yaje ya zauna snn yace"Mae lesson d'in wnn yrnyr ne" Itama zama taje tayi kusa dashi tace"hm wlh ni nama d'auka ko mami ce akeyiwa lesson kullum ashe wnn abar ce,gsky Abban nn naka mutum ne mai takurawa don nsn duk shine ya matsa maka akan haka. Yace"to kar dai kiyi gigin fad'ar banzar magana wa Abbana" Ta kwanto mae tare da fad'in"nama isa kawai dae na tsani yrnyr ne wlh,wae ace ga er gida ba'ayiwa lesson ba sae ita, yace"itama ai za'a fara yi mata ne,yau ma naso ace an fara mata sae gashi bata nn " ina ta tafi ne ko sun fita ne itada wnn abar? Yace" tabi inna ne" Ta d'an yamutsa fuska tace"waye kuma inna?kallon kin raina ni ya mata tace" oh kakar ka ko na manta ne amma kuma me ya kawota?Yace"dubiya"waye ba lfy badai kai ba" Yace"wnn yrnyr ce" Allah yasa ta mutu kowa ma ya huta, da sauri man ya kalleta tace"eh gsky na fad'a ai don ko bata mutu ba ni sae na zamo ajalinta,don ba'ayi macen da zata ra6eka ba wlh ni kad'ai ce ba qari" Shiru yayi kmr ma baya jinta sae danne danne yake a wyrsa. Washe gari ta kasance Monday Rynt ce ta fito harabar gidan sanye da uniform d'in ta. Ita kad'ai ake jira don har mami ta shiga mota shiyasa sae son take tayi sauri amma kuma bazata iyaba sbd har yanzu gurin na mata ciwo wacce duk ta taka qafarta sae ta qara jin tsanar man a cikin ranta. Tun lokacin da ta fito man ke kallonta wanda ke zaune kan resting chair riqe da jarida yana karatu yana shan iska. Samun kansa yayi dajin tausayinta sosai har dai da ya tuna yanda abin ya faru tsakanin shi da ita wanda har yanzu yana matuqar mamakin kansa da kusantar ta da yayi,haka kuma yana jin haushin kansa. Ajiye jarida yayi ya nufo gun Rynt wacce tana ganin sa tafe ta kauda kai ta kuma tsaya cak ta daina tafiya, har ya qaraso gab da ita ya tsaya nn suka kalli juna hkn yasa man ya hango tsantsar tsanar sa a cikin idanuwanta. Da sauri Rynt ta kauda kanta gefe haka shima Snn yace "bazaki iya zuwa school d'in nn ba kiyi zamanki kawai har kiji sauqi. Daga hk ya juya yace da driver"tafi kawai ka kai mami" Rynt kmr zatayi kuka tace muna da test ne fa" Kallonta yayi a natse yace"naji amma muje ciki ayi maganin matsalar tukun sae na kaiki school" Shaye da toka tace"bana so" Daga haka ta ra6a ta gefen sa zata wuce yasha gabanta tare da Fad'in "bana son raini muje ciki nace kuma idan kika musa min wlh sae nace mkrntr ma baxa ki je ba! Komai bata sake cewa ba sae kuka ta fashe mai dashi yaja hannunta ya tafi da ita sae d'akinta. Sae da ya sake mata hannu snn ya shiga bathroom ya had'a ruwan zafi da dettol ya fito ya sameta tsaye inda ya barta sae kukanta take. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [9:40PM, 1/29/2017] Billy giro😊: 29/1/2017 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 🔮🔮🔮 *page* *38* Yace"wae kukan name to! Tace"na gaya maka test mukeda kuma malamin idan akayi letti duka yake kuma baya bari a shiga aji har sae ya fita" tana maganar ne cikin muryar kuka . Yace"oya shiga bathroom zaki samu na had'a ruwan zafi ki shiga ciki ki gasa jikin ki" Tace"Dan Allah kabari idan na dawo wlh bana son ayi test bana nn" Bai kula ta ba sae kan sofa yaje ya kwanta snn yace "idan kinga dama kije ki gasa jikin naki idan kuma tsayuwar zakiyi tayi to. Daga nn ya rufe idanuwan sa Rynt kuwa wani takaici ne ya kawo mata iya wuya,ita ba don tana son bokon nn ba da ba abinda zaisa ya kama yi mata abubuwa hk ta barshi. Haka ta nufi toilet tare da fashewa da wani irin kuka na takaici tana maganganun da ba'a jin me take fad'i,wacce tana shiga bayi ta rufo qofa da qarfi kuma sae jin abubuwa kake suna ta 6irari ga dukkan jefar dasu ne take. Sae a snn mohd ya bud'e idonsa ya koma rufewa,jin ihunta yasa shi saurin tashi yaje bakin bathroom d'in yace"lafiya"tace"to ai ruwan ne da mugun zafi baka gaya min ba" Yace"sae na gaya miki ke bazaki ta6a ruwan ba kafin ki shiga" Uhm Uhm wlh Allah kayi min mugunta. Tsaki kawai yayi yace "kinga kiyi sauri ki sirka ki fara abinda nasaki ,ni ina da abin yi idan ba hk ba zaki fito ki samu bana nn" Daga haka ya koma yayi kwanciyar sa. Bata wani jima sosai ba ta fito gudun kar ta samu baya nn , ba tare da ya bud'e idon sa ba yace"har kinyi me? Har na gama mana,to koma ki sake zama,tace"haba dan Allah kaifa kace nayi sauri" Yace ke kika sani jikin ki ko nawa. Daga haka ya tashi ya fita tabi bayan shi wacce yanzu har sauri take had'awa dashi sbd jikinta duk taji ya sake mata ba wani ciwo sosai d'in nn. Bayan en wasu kwanaki da faruwar haka. gabad'aya Rynt ko gaida man ta daina yi asali ma in ya shiga d'akinta kmr ma bata ganshi ba takeyi haka shima mami kawai yake kulawa. Karatun ta kawai ta sa ma gaba sae dai a duk lokacin da ta tuna cewa wani abu ya shiga tsakanin ta da man sae ta zubar da qwallar baqin ciki,taji inama rayuwa zata koma baya da rnr bata je gyra mai d'aki ba. D'aki take ta dawo daga mkrnta kenan ta ajiye jaka snn ta cire hijab,d'ankwali da takalmi da kuma socks ta kalli mirror taga gashin kanta duk ya taso ta cire ribbon sae ga mami ta shigo da gudu tare da cire school bag d'inta ta jefar haka hijabinta da takalma sae kuma ta fita da gudu abinta Rynt ta d'auke kayan ta kaisu duk inda ya dace snn ta taje kanta ta shiga bud'e buttons d'in rgrta ,ta bud'e na farko da na biyu sae kawai taji ihun mami. Ba shiri ta fito da gudu don ta d'auka ko wani abu ne ya same ta sae taga ashe pretty ce tazo shine take ihun tarbonta. Rynt ta d'an saki fuskarta ta gaida pretty wacce tayi kunnen uwar shegu da ita,Rynt ta qara gaida ta indà cikin daka tsawa pretty tace"da Allah ni kin cika min kunne bana buqatar gaisuwar ki dole ne! Rynt ta kauda kanta zata juya ta bar gurin sae ga man ya fito shida malika,pretty ta gaida man yayinda malika taje da murna gun pretty tana fad'in"oyoyo mamn twins ya tsufa, pretty ta ta6o tulun cikinta tace"wlh gashi nn muna fama dashi ita kuma er iskar yrnr nn ta wani zo tana cika ni da gaisuwa sae kace don ta nazo" Malika ta ta6e baki tare da kallon Rynt tace"kinsan matsiyata sun fi kowa baqin shisshigi da cusa kae ba farin jini" Wlh kuwa kmr kin sani cewar pretty wacce malika taja ta zuwa 6angarenta yayinda mami ke biye dasu. Rynt kuwa bata bar zuciyar ta taji zafin mgnr su ba sae juyawarta tayi zata koma d'aki tare da jin hausin kallonta da taga man nayi,wanda ba don komai yake kallonta ba sae don ganin yanda yalwataccen gashin ta ya sauka har kafad'unta, ba kmr na malika ba dako kan wuyanta bai kawowa shiyasa kullum take fama da sa na kanti. Har Rynt ta fara taka matattakala ne taji sallamar nasir tare da fad'in "ah Rynt"fuskarta wasae ta juyo tace"na'am yaya nasir ina yini yace"lfy lau ya mkrnta? bata riga ta amsa ba taga man ya dalla mata muguwar harara had'e da kallon qirjinta, a kafaice ce ta kalli qirjin nata wacce sae a snn ta tuno yanda ta fito ba hijab ga buttons d'in rgrta da ta fara bud'ewa amma ba'a ganin komai sae white vest d'inta wacce ko ita kad'an ake hangowa. Ai kuwa da sauri taba nasir amsa ta wuce. Su Malika kuwa suna shiga d'aki pretty ta kalli mami tace"mami jeki ki cire uniform kici abinci sae kije gun yaya nasir ya siyo miki ice cream ko. mami ta fita d'akin da murna yayinda pretty tayi saurin bud'e jakarta ta ciro wani qullin magani ta bawa malika tace"umma ce tace na kawo maki kisa ma wnn matsiyaciyar yrny a abinci taci ta haukace tabi duniya. Malika ta kar6a fuska a yatsine tace"nifa ba iya abubuwan nn nayi ba"pretty tace"ai kuwa shiyasa gata nn har yanzu kin kasa ftr da ita abin haushi har shi kanshi yaya dako yaushe yaso rabuwa da ita zai iya amma shiru kmr an shuka dusa"malika tace"hm ni kaina abin na ban mamaki da haushi wlh" pretty tace"yo kina tunanin a banza tabarshi ne wae ace tun auren ku umma ke fushi dashi akanta amma still yaqi rabuwa da ita ai kinsan ba a banza ba wlh,dashi har Abba ni ban yarda cewa ba wani abu tayi musu ba. Malika tace"that's y ba'a banza ba kenan shiyasa naga an sanyata a tsadaddiyar mkrnta har ma wae ana mata extra lesson a gida" Pretty tace"to kin gani idan zaki tashi tsaye ki tashi tsaye don wata rana baki da kwanan ceto zata qwace miki miji kizo ki zama er kallo har dai idan ta fara hayayyafowa......tuf! bari zancen nn dan Allah da wane matsayin nata zai fara kula ta har takai ga fara haifo 'ya'ya. Pretty tace"kina sake da baki kuwa duk hkn zata faru don gashi yanzu kece ke baki iya aiki da irin wnn maganin ba" To gaya min yanda zanyi inji, pretty tace "kmr dai yanda na gaya miki a abinci zaki saka mata da zarar taci ko lomo d'aya ce tofa hauka tubran,few! kuda sake jin lbrnta sae dae ko a lafira, malika tace"aike matsalar kuku ke dafa mana abinci kuma har dakin ta yake kai mata nata abincin, but zan san yanda zanyi bcs man zaiyi tafiya a kwanakin nn byn ya tafi zan sallami kuku , dolenta zata fito zuwa girka abinci da haka zan fake tana d'agawa zanje na zuba mata shi a abinci,idan man ya dawo bae sameta ba ce masa kawai zanyi tun rnr da kayi tfy itama ta sa qafa ta fita. Pretty ta kwashe da dariya had'e da bata hannu suka tafa. Bayan kwana d'aya da faruwar haka man ne zaune a tsakiyar gado ya lanqwashe qafafu yana aiki da laptop sae ga malika ta shigo d'akin riqe da kofin coffee a hannunta kan gadon ta hau taje close to man tayi irin zaman da yayi tana mai kallon aikin da yake a laptop ta miqa mishi coffee tare da fad'in gobe ne tafyrka ko? Sae da ya kar6i coffee ya kuma yi kur6i d'aya snn yace"eh ko kina zuwa? Tace"Aa" Yace"en son yawon basa kai kenan"tace"hakane kam sae dai idan zakayi wata tafiya xan bika" Kallon ta kawai yayi yaci gaba da shan coffee d'insa. Tace zakayi sammako ne? Yace"sosai kuwa da wani abu ne ?um um ba komai. Sukayi shiru can malika ta kalle shi ganin yanda yake ta kallon fotunan yara kyawawa, dama tasan aikinsa ne kullum sae yayita searching d'in pics d'in yara yana kallo" Cikinta kawai taji ya shafo ya kalleta yace"malika ina son yara sosai amma naga kmr ba kya son haifo min" Murmushi tayi tare da shafo gefen fuskar shi tace"zan haifa mana nawan kasan ina son abinda kake so" yace"ina son yara da yawa amma Abbanki bazai bar mu ba,hancin sa taja tace"abu mai sauqi se na haifa maka en uku a lokaci d'aya kmr ku"yayi murmushi yace"da kinci babbar kyauta kuwa tace"Allah"yace"dgske"tace "kmr me kenan?yace"sae abinda kika ce kina so"tace"wow har na qagu naga na samu ciki" yace"na fiki qaguwa da hk"tace"a daa kenan amma yanzu na fika" Yace"dsgske to meyasa?ta bashi kiss snn tace"sbd ina sonka da yawa kuma xan so ko yaushe na ganka cikin farin ciki " "Uhm"shine kawai abinda yace yaci gaba da shan coffee yana kuma ci gaba da kallon fotunan yara. A sha biyu na daren rnr ne mohd yaje d'akin Rynt ya samu sae bacci suke ita da mami, kowaccen su na sanye da riga da wando na bacci ga littafai watse akan gadon ga dukkan alama baccin kwasar su yayi basu kammala abinda suke ba dan har ma biro ya hango riqe a hannun Rynt,a hnkli ya zare biron yana mai kallon fuskarta snn ya tsince kaf littafan ya d'aura su akan bedside drawer yayi tsaye yanata kallon Rynt bako qyaftwa sae itace ta motsa tare da juya mai bayanta amma duk cikin bacci ne bawai don tasan yana tsaye ba. Numfashi ya fitar a hnkli yaje yaja blanket ya rufe musu jikin su sbd yanda yaga yanayin kwanciyar Rynt da kmr sanyi take ji. Sae da ya kashe musu wuta snn ya rufo musu qofa ya fito. A washe gari tunda safe kuwa man ya tafi. Ko breakfast malika bata bar kuku ya had'a ma mami ba ta sallame shi a gaban su Rynt don kawai Rynt tasan anjima dole zata fito d'aura girki. Hkn yasa ta riqa kud'in breakfast har da mami. Da yamma su Rynt sun dawo school a gjya amma hkn ta jure ta fad'a kitchen ta d'aura musu taliya snn ta koma d'aki dmn ta d'an watsa ruwa. Dama malika na zaune a falo tana ganin wucewar Rynt ta nufi kitchen ta bud'e girkin ta zuba garin maganin kaf ta motse ta rufe snn ta fito. Taje har d'akin Rynt ta jawo mami tace"muje kici abinci"tace"ai Anti ta d'aura mana abinci malika tace"wanda zan baki yafi wanda take dafa muku dad'i ko ba kya ci?tace"ina ci" Bayan sun fito mami ke cewa "anti ina son zan d'auko teddy na a d'akin yaya " tace"to muje ki d'auko" Bayan sun fito ne suka tafi d'akin malika ,malika bata bata abincin ba sae waya ta shiga yi bayan ta gama ne ta d'aukowa mami ragin abincin ta da taci mami ta kalli abincin a yatsine tace"anti aini bana cin ragi tace"don ubanki da kike cin ragin yayanki fa! To anti yaya kika ce...iyye lallai ma yrnyr nn oya ftr min a nn! daga ma naso taimakon ki!mami ta wani turo baki tana kallonta snn tabar d'akin, malika ta buga tsaki tare da kwanciya kan sofa tana fad'in"Allah yasa har kema kici abincin duk ku haukace ni ba ruwana. Mami kuwa d'aki taje bata sami Rynt ba ta fito sae wasa take da qatuwar teddyrta ta nufi kitchen ta samu dai dai Rynt ta gama zuba abinci a tray ta juyo riqe da trayn a hannun ta. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [10:39PM, 1/30/2017] Billy giro😊: [ 1/30/2017 ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮``` 🔮🔮🔮🔮 *page* *```39```* Girshi Rynt ta ga mami close to her ga kuma teddyn da ta gani a hannunta hkn yasa ta buga razanannen ihu had'e jefar da trayn hannunta. kafin trayn yakai qasa ita kuwa mami ta fasa nata ihu tare da jefar da teddy sbd yanda taliya ta watso mata a hannu a rikice Rynt tayi kanta tana cire mata taliyar ita kuka mami kuka sbd har ftr gurin ta d'an kwaye ya kuma yi ja sosai. D'aki suka je amma gabad'aya Rynt ta rasa natsuwarta don mami sae kuka take tayi. gashi tasan cewa man baya nn wacce taji hkne a bakin malika da zata sallami kuku hkn yasa ta yanke shawarar zuwa gidan inna. Hijabi kawai ta zira ta d'auki mami suka tafi. Bayan har sun wuce ne malika ta fito cike da murna don a lokacin da su Rynt sukayi ihu har kunnenta yaje sae ta d'auka ko ihun hauka ne ta jiyo sunayi. Ta tafi kitchen ta same shi kaca kaca tray yayi nasa gefe taliya ma haka da kuma teddyn mami,nn ta kwashe da wata irin dariya tace"lallai aiki yayi kyau kmr yankan wuqa wata qil loma d'aya kawai sukàyi amma har sun bi sun haukata kitchen hk yanzu koina suka nufa ne oho Allah yasa ma sufi ruwa gudu" Daga nn ta tafi d'akin Rynt don ta qara tabbatarwa kanta ta samu kuwa koina basa nn har bathroom, farin ciki taji fal har ranta don sae kwasar dry take tana fad'in"matsiyaciya bake ba mijina har abada kai ko a lafira wlh, bari ma na kirashi naji ko ya isa lafiya. Nn ta kira man suka jima suna waya cike da nishad'i byn sun gama tasa aka gyare kitchen tsaf ta kuma kira kuku a cewar ya dawo yaci gaba da aikin sa. Sae a bayan snn ta kira pretty ta gaya mata sae dariya suke ta kwasa. Sae dai bata snr da ita cewa har da mami ba. Rynt kuwa suna zuwa gidan inna suka sami nasir a can shine ya d'auki mami suka je asibiti akayi treatment nata suka dawo. Da yake inna tasan mohd yayi tfy tace da Rynt suyi zaman su har sae idan ya dawo sae su koma,har ma take cewa nasir yaje da Rynt gidan ta d'ebo musu en kyn sawa, hkn kuwa yayi ma Rynt dad'i sosai duk da bata san ko kwanaki nawa man zaiyi bai dawo ba. Da byn sllr isha'i ne suka je gidan Rynt ta d'ebo musu kayan sawa ita da mami sae dai bata had'o musu da uniform ba sbd an kusa shiga weekend kuma ta fiso sae mami taji sauqi snn ko zasu koma sbd ba wani sosai d'in nn ta qone ba. Shigar su gidan har fitowar su basu had'u da kowa ba sae mai gadi kad'ai. Bayan sun koma gidan inna ne nasir ya koma gida ,pretty tazo da murna ta tarbe shi ta kuma kawo mishi abinci ,ba kmr kullum da sae yace takawo mai take kawowa ba. Zuba mishi abinci take har ta gama idonsa na kanta ,sae da ta zauna ne yake cewa"wae yau wane irin farin ciki ne kike ciki haka naga har bakin ki baya rufuwa,kallon sa take tana murmushi tace"ba komai kawai dai kati nake so zan kira umma,tun d'azu nake jiranka da kace zaka turo min naji shiru. Nn yasa hannu a aljihu ya ciro kati ya miqa mata snn yace "kwata kwata mantawa nayi wlh"tace"to ngde"snn ta tafi d'aki ta sanya kati ta kira ummarta tana gaya mata lbrn da malika ta snr da ita,umma tace"da kyau qwarai kaddai ki sake Nasir yaji tace" haba ina hauka ne umma aini bana son kowa ma yaji har sae tayi nisanda ba'a iya gano ta ,umma tace"ai ta tafi kenan ba dawowa er matsiyata taje can ta qarata ba ita ba d'ana bare a tatse min shi" pretty ta kwashe da dariya tace"umma zan kiraki anjima naji nasir na qwala min kira. Nn suka katse wyr ta tafi gun kiran nasir da ta samu ruwa ne yake buqata. Bayan kwana biyu da fauruwar hakane da yamma sosai man ya dawo daga tafiyar da yayi. malika ta tarbe shi sae murna take tana wani nn nn dashi don kawai ta samu ta mantar dashi komai sbd bata son yayi saurin gano su Rynt basa gidan har dai mami da ta kasance abokiyar cin abincinsa. Shi kuwa a gjye ya dawo shiyasa sam bai leqa d'akin Rynt ba sae a washe gari da ya dawo sllr asuba ya shiga bai gansu ba,yaje koina a gidan basa nn . Da mamaki yaje yana tmbyr malika cewa ina wnn yrnyr ta tafi tunda safe haka?ta6e baki tayi snn tace"oho kawai dae tun rnr da kayi tafiya itama tasa qafa ta fita"yace"tasa qafa ta fita kuma shine har yau bata dawo ba,d'ibar kayanta tayi ta tafi dasu ko yaya? Oho ni ina zan sani Yace" lallai yrnyr nn ta raina ni da yawa wlh" Daga hk ya wuce d'akinshi rae 6ace ,malika kuwa ta bishi da ido ta6e da baki. Sae guraren 11 man ya fita gidan bai zarce koina ba sae gidan inna. Ya sami inna, nasir, Rynt ,da kuma mami a nn harabar gidan sun fito zasu shiga mota. Yana fitowa mota mami taje da gudu ta tarbo shi ya riqo hannunta suka qaraso gurin su Rynt . Bayan sun gama gaisawa shida nasir da inna har suna mai ya hanya yace dasu alhmdlh snn yaje gab da Rynt ya tsaya yana mata kallon tuhuma,sau d'aya ta kalle shi ta sadda kanta qasa. Mohd ya maida duban sa gun inna yace"inna me yrnyr nn taxo yi a gidan nn?tace"ayyo ai da baka nn ne tsautsayi ya sami mami ta qone a hannu duba ma kaga ga hannun nn ta fad'i hkne had'e da riqo hannun mami ta nuna mae ya duba hannun yaga qonuwar ba sosai bace kuma har ta soma warkewa dan kad'an ma ya saura, yace"garin ya hk ta faru, Rynt ce tayi mae bayani inna ta d'aura da cewa shine nace suyi zaman su har sae ka dawo tukun tunda ba mae kula dasu can, yace"haba inna ai ko nasir mai zuwa yana duba su ne ba sae kin wani ce su zauna a nn ba" Inna tace"yo kai Muhammadu kai kafi son kullum mutum yayi ta zama qunqushe cikin gida baya fitowa yaga en uwa" A d'an qufule yace "shike nn inna naji yanzu ina kuma zuwa kun wani kwaso ku duka haka" Sae da inna ta washe baki snn tace"wae zamu tafi ne gurin su saliha kasan yau ake bizitin " yace"inna haka ai sae ku cika musu mkrnta ku kuje gida ma suje haba kar kusa a d'auke ku gidadawa mana.....yo muhammadu alqawari fa na musu akan zanje ko so kake na karya? Yace"bance ba amma dae bazaku je da wnn yrnyr ba"ya fad'i hkne tare da nuna Rynt wacce tayi saurin d'agowa ta kalle shi yayinda inna ta gwalo ido cike da masifa tace"kan me! yace"kuje kawai ni zan kawo ta daga baya" Inna tace"bakaji da kyau ba tare dae zamu tafi" Nasir yace"Aa inna wata qil akwai unxurin da yake da shine" Tace"yo kai baka san hln muhammadu bane, ba wani uzurin da yake da hana mata tfyr kawai yake sonyi" Nasir yace" inna kawai dae muje tunda yace zai kawota d'in ai zai kawota" Inna bata wani gamsu sosai ba amma hk tayi sallama da Rynt a cewar sae sunzo. Daga nn suka shiga mota ita da nasir har mami. Rynt kuwa ta kalli man idonta tap da qwalla sbd tasan hanata zuwan ne yayi,kallonta yake ta kauda kanta cike da son ta fashe da kuka amma ta danne sbd mami da taji ta qwala mata kira tana mata bye bye nn ita ma ta shiga yi mata bye bye har motar su tafita ta sake kallon man tare da fashe mai da kuka marar sauti,ta shiga roqon dan Allah yayi hqr ya barta taje bai kulata ba sae hannunta yaja zuwa mota tirje mai take amma haka ya d'ura ta mota ya rufe sae jin yayi ta fasa ihu yayi saurin bud'e gambun yana tmbyrta lafiya ? bata iya bashi amsa ba sae fitowa tayi ta fad'i nn qasa riqe da qaramin yatsanta na qafa sae kuka take tana yawo da qafar ,man ya rikice yana tmbyr mene ne wae tace"wani abune ya cije ni..... What bana son qarya fa a motar tawa! Tace"wlh Allah kuwa ka duba zaka ga koma mene ne, ba musu yaje yana duba motar tashi da ta kasance tsaf tsaf sae kawai yaga kunama ai kuwa da mugun mamaki yake ci gaba da kallonta yana kuma mamakin ina aka shigar mae da mota da baya nn har kunama ta sami damar shiga ciki kaddai d'an iskan driver ya samu mai shigar mae da mota koina ya samu,tsaki ya buga had'e da ciro takalmi ya kashe kunamar snn yayi kan Rynt da sauri ya cire necktie d'insa ya d'aure mata yatsa ya samu da qyar ta shiga motar don sae kuka take ita bazata sake shiga motar ba. Bayan ta shiga motar yaja motar da sauri sae chemist aka mata allura a yatsar aka kuma bata magani snn sukayo gida wacce koda suka iso gidan tuni Rynt tayi bacci da kanshi ya d'auke ta ya shiga da ita gidan yayi kici6is da malika zata fita. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [10:32PM, 1/31/2017] Billy giro😊: [ 1/31/2017] ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮``` 🔮🔮🔮🔮 *page* *```40```* Waya malika keyi bata san lokacinda wyr ta sa6ule a hannun ta ta fad'i qasa ba. Bata damu da kula wyr ba sae kallon Rynt take da mugun mamaki tace"kai! me zan gani! kan uba! badai wnn abar ce nake gani ba kuma d'auke a hannun ka! Kallonta kawai mohd yayi ya ra6a ta gefenta ya wuce, bai zarce koina ba sae d'akin Rynt yayinda malika ke biye dashi cike da masifa tana mae tambayoyi ,sae da ya ajiye Rnyt snn ya jawo hannunta suka baro d'akin suna saukowa downstairs ta wani fizge hannunta da qarfi snn tace"kamin bayani nace a ina kaganta ne wae!da har zaka wani tallabota haka! Yace"ha'a! a ina kuwa banda gidan inna! Da mamaki tace"gidan inna kuma?yace"eh mana da to ina zan ganta a tunanin ki? A d'an daburce tace "dole nayi mamaki mana byn nsn.....sae kuma tayi saurin katse kanta da cewa"abinda ma yafi d'aure min kai shine ya akayi ka tallabota wae? Yace"bacci tamin a mota....what!amm kaji kunya wlh ai ko gawa ce wlh bai kamata ka zamo d'aya daga cikin masu tallabar gawar ba bare wae don ta ma bacci a mota iyye lallai wlh na yarda yrnyr nn ba'a banza ta bar ka ba! Tsaki kawai ya buga ya fita yana qwalawa drivern sa kira. Da sauri driver ya qaraso gare shi man ya kalle sa a fusace snn yace"dan gidanku ina ka shigar min da mota ne da bana nn yace"wlh koina ban shigar ma da mota ba yalla6ai!mohd yace wlh idan kamin qarya a bakin aikin ka tayaya to zan sami kunama a mota ta ka wani cemin bakaje da motar koina ba! Driver yace"wlh na rantse yalla6ai ba inda naje da ita amma kuma nayi mamakin da kace ka sami kunama a ciki sae dae kuma gsky nasan jiya da dare na wanke motar har ma na shanya car mats akan flowers kuma gskyr magana da suka bushe ciro su kawai nayi na maida mota ba tare da na kakka6e ba don ban ko kawo cewa wani abu zai hau akai ba,nn kawai mohd ya shiga qwalawa baba mai gadi kira, wani dattijo yazo da sauri zai durkusa mai, mohd yayin saurin cewa"a'a basae ka durqusa min ba ina so zan kora ma bayani ne akan flowers d''in gidan nn ,bawai aikinka kawai ka riqa basu ruwa ba, har tsaftar su sae ka kula da ita inace har maganin qwari sae da na siyo na baka wanda ga dukkan alama baka amfani dashi Baba, wlh haka ne yaro amma zan kiyaye daga yau ayi hqr,mohd yace"kaga Baba idan har kasan baza ka iya kula da flowers d'in nn ba kawai ka tsaya a iya gadinka na samo wani wanda zai kular min da flowers" Baba maigadi yace"yaro wlh nayi ma alqawarin zan kula dasu yanda kake so" Yace"to baba yanzu kaje ka saka maganin da na baka snn ka share duk wani datti dake qarqashin flowers d'in yace "to shikienan"ya tafi cikin hanzari yayinda man yace"da driver kai kuma kaje ka bud'e boot d'in motar ka ciro wnn car mat da na kashe kunama akai ka wanke shi tas snn itama motar ka bincika min ita da kyau ka kuma sake wanke ta then ina warning d'inka akan kar ka sake maida min abubuwan mota haka kawai ba tare da ka kakka6e ba idan ba hk ba wlh a bakin aikin ka . yace "inshaAllah yalla6ai an gama" Nn mohd ya juya ya koma cikin gida. Malika kuwa lokacinda man ya buga tsaki ya fita taji kaman ta fasa ihu don takaici ga kuma tsananin mamakin da take d'auke dashi na ganin Rynt bata haukace ba kan dole ta duqa ta d'auki wyrta taje d'aki ta kira pretty ta gaya mata abun mamaki da haushi da suka faru da ita yanzu, pretty tace"abin da d'aurewar kai wae ma kin tabbatar taci abincin kuwa? Hm pretty ina d'aki fa na jiwo ihunta kuma koda nazo na sami kitchen duk a hargitse na kuma duba koina a d'akinta bata nn"pretty tace"me man yace miki taje yi a gidan inna? Ni ina naga natsuwar tmbyrsa haka don wlh ji nayi kmr zuciyata zata fashe a lokacin da naganshi d'auke da ita gani kuma d'auke da mamakin ya akayi ya samota don tuni na gama sata cikin jerin shafaffin mutane sae dai kuma a lokacinda na ganshi d'auke da ita nayi tunanin ko tsinto ta yayi garin haukarta shine aka mata allurar bacci,wae sae yace min bacci tamai a mota,pretty tace"kinsan hln yaya da baqar magana amma kuma dole idan taci wnn abinci sefa ta haukace kuma baxa a ta6a samota ba sbd qa'idar maganin kenan but yanzu kije gun yaya cikin hikima da nuna komai ya wuce a gurin kiji shin me taje yi gidan inna da har tayi kwanaki bata dawo ba,malika tace shikenan i will call u back idan nayi hkn. Nn suka katse wayar ta nufi d'akin man ta same shi zaune kan sofa ya tasa 'ya'yan fruits gaba yana sha. Taje gab dashi ta zauna ya kalle ta sau d'aya ya kauda kai. Hannun takai ta juyo fuskar shi saitin fuskarta yayinda ta qirqiro hawayen qaryanda suka cika mata ido tap inda cikin muryar kuka tace"my man na fhmci ka daina sona kwata wata yanzu wnn abar kake so" Ajiyar zuciya ya sauke yana mai kallon yanda hawaye suka fara sauka akan kumatun ta yace"malika ta yaya kike tunanin zan daina sonki naso wnn abar da kwata kwata kinsan ita ba tsarina bace" Tace"idan baso ba to meyasa don tayi bacci zaka wani d'aukota ai tashin ta ya kamata ace kayi,malika nifa tausaya mata kawai ne nayi sbd allurar baccin da take d'auke da ita, Allurar bacci kuma?eh kunama ce ta harbe ta shine da muka je chemist nasa aka had'a mata har da allurar bacci,amma ai gwanda kabarta a motarka idan tafarka ai ta shigo da kanta dn sam ba ajinka bace a ganka d'auke da ita,yakai hannu yana share mata hawaye yace"naji abar zancen ya wuce" Nan ya rungume ta sukayi shiru sae can malika ta kalle shi tace"hln me taje yi gidan inna da har ta kwana biyu ko inna ce ba lafiya? Yace"mami ce ta qone a hannu "garin me? Nn ya gaya mata bayanin da Rynt tayi mae tayi tsaki a ranta wacce a cikin ran nata take cewa _"matsiyaciya bata ci ba kenan ai da na nasn hk zata faru da bazan bar mami ta tafi ba"_ Nn ta buga tsaki a fili zata fita man yace"yadai lafiya? Tace "haushi ta ban ne wlh in banda gidadanci teddy ce abin tsoro da har zata 6arar da abinci har ta kai ga qona mami" Kallonta kawai man yayi yakai hannu kan wyrs da ta shiga ruri ya d'aga ita kuma ta fita taje d'aki ta kira pretty byn pretty ta d'aga tace"ke ashe matsiyaciyar bata ci abincin ba 6arewa yayi har ya sami mami a hannu ta qone shine suka je gidan inna"pretty tace"haba kam ni nsn idan taci sae dai wata ba ita ba,amma kar ki damu yanzu zan kira umma na gaya mata ta kar6o miki wani,malika tace"to shike nn bye tank u" Ta katse wyr had'e da tsaki tana fad'in"niko kun sake kawo min maganin ba aiki zanyi dashi ba tunda har ana iya gujewa sharrin sa amma nawa sharrin ko waye ubanta tayi kad'an ta guje mishi wlh. Mtsalar kawai ban san yaushe zan sami ciki ba ga man Dr ne bare na iya cikin qarya har na cimma burina bai gano ni ba....qarar wyrta ne ya katseta ta d'aga wyr had'e da shiga bathroom Rynt kuwa tun lokacinda da man ya ajiye ta take bacci har akayi zuhur bata farka ba. Man ne ya shigo d'akin wanda ya fito daga masallaci kenan yaje gab da ita ya zauna yana mae duba yatsar wanda yana kai hannunsa akan yatsar ne Rynt ta farka had'e da tashi zaune snn takai idonta akan yatsar da take d'an d'auke da kumburi, man yace"har yanzu kinajin zafin harbin ne? Ta girgiza mae kai snn tace kawai dai allurar tana min zafi" yace"tashi kije kiyi sallah zai daina ne" Ba musu ta tashi ta nufi bathroom inda kallonta yake har ta shige bathroom d'in snn ya tashi ya bar d'akin. Tun daga lokacin bai sake komawa d'akin ba sae a washe gari da safe su Rynt na shirin school ita da mami sae ga man ya fad'o d'akin Rynt tayi kmr bata ganshi ba sae jin tayi ya jata ya zaunar ya durqusa had'e da riqo qafarta yana duba yatsar ya kalleta snn yace "kumburin ya sauka kenan ? Ta gyad'a mai kai tare da yunqurin tashi ya maida ta had'e da fad'in "zafin allurar fa?shaye da toka ta kalle shi kmr shima yanda yake kallonta ta kauda tata fuskar snn tace"ta daina min zafi" Nn ya tashi tsaye ya kalli mami da taxo gurin shi tana fad'in"yaya amma yau kae zaka kaimu school ko?um um mami driver dae zai kaiku,uhm uhm pls yaya ka kaimu kar amana bulala kan kwanakin da mukayi bamuje ba kasan inna ta gaya ma kuma idan ba'ayi musu bayani ba zasu dake mu ne,yace"to shike nn idan kun shirya ku sameni a downstairs,tace"to yaya yanzu da mun gama shiri zamu zo" Nn ya fita sukuwa suna gama shiri suka je suka sameshi yakai su school. Bayan wata d'aya da faruwar haka Alhmdlh komai na bi dai dai yanda Rynt keso na harakar karatunta wacce ashe kwanyar ban mamaki ce da ita don qwarai qoqarinta ya shiga bayyana sbd duk wata test ko Assignmen kaf take lashewa haka ma class duk wata tambaya da malamai keyi ita ke farkon bada amsa , Kan qoqarinta ne wani malami yake mutuwar sonta sbd kaf makarantar ba wanda yasan ita mtr aure ce har frnds d'inta kuwa. Kullum idan taje school sae ya aika a kirata amma bata zuwa, ba yanda bai yi ba ya samu ta kulashi ko sau d'aya ne amma fir taqi. Rnr wata alhamis yayi aike har ya gaji taqi zuwa kan dole yaje da kanshi har class d'insu ya samu tana wani Assignment yaje kan desk d'inta ya d'aura hannyensa akai had'e da russunawa yana mata magana cikin yanayi na kmr wanda ke duba mata Assignment d'in itakuwa tayi kmr bada ita yake zancen ba sbd dama tsanar sa take tun farko dmn kowa ya sanshi makarantar d'an iska ne kuma mugu. Da yaga taqi kulashi ne ya kar6e Assignment d'inda takeyi ta tashi a fusace cikin d'aga murya tace"kaga malam nifa ba irin en matan nn bace don hk ka daina bibiyar rayuwata haka nagaji!" Mgnrta ta tinzirashi sosai musamman da yaga students duk hnklin su yayo kansu nn yasa ta kneel down ya nemi bulalar dorina sae zabgarta yake har sae da ya gaji don ganshi yabarta sae kuka take en class na bata hqr a cikin haka ne aka buga tashi wacce har aka zo d'aukar su suka isa gida kuka take ta tafi d'aki aguje zata fad'a kan bed sae jin tayi kawai an fizgota koda ta duba man ne yajata zuwa jikin shi , sosai taso qwatar kanta amma ta kasa sbd riqonda ya mata kan dole ta fad'a kan qirjinsa ta fashe mai da wani sabon kuka. A hnkli ya kai hannunsa ya jaye hannuwanta da tasa a tsakanin qirjinsu ya shigar da ita gabad'aya cikin qirjinsa yana mai tmbyr abinda aka mata,saurin ture shi tayi daga jikinta ta nufi bathroom da gudu. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:41PM, 2/1/2017] Billy giro😊: [ 2/1/2017] ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮``` 🔮🔮🔮🔮 *page* *```41```* Ta rufe qofa tare da zamewa jikin qofar ta had'e kai da guiwa tana ci gaba da kukanta. Mohd kuwa juyawar sa yayi zai fita d'akin sae ga mami ta shigo riqe da hijab, school bag, da takalmi da socks ta jefarda su kan sofa ta riqo hannun sa tare da kallon fuskar sa snn tace"yaya anti ta gaya maka me take ma kuka? Yace"bata gaya min ba ko kinsan me take ma kukan ne" um um nima ban sani ba kawai na ganta tana kuka" Bai sake cewa komai ba sai hannunta yaja suka tafi downstairs ya kira kuku ya kawo abinci plate biyu mohd ya kar6a yaba mami d'aya ya tashi ya nufi d'akin Rynt da d'aya. Wanda yana shiga d'akin yaga giftawar Rynt ta koma bathroom, ya ajiye abincin yabi bayanta . Yana tsaye ta cire hijb da riga takai hannu zata cire vest kenan ta hango shi ta jikin mirror ai kuwa ta buga ihu had'e da kare qirjinta ta duqe qasa tana fad'in ya fita! bai fita ba sae bayan banta yake kallo da duk ya kasance d'auke da shatar bulala,rai 6ace ya tayar da da ita tsaye ya juyota yana kallon fuskarta snn yace "wane d'an iskan malami ne ya dake ki haka! Shaye da toka ta sake juya mai baya tace"to ni ka fita ai zan zo na maka bayani ne" Fixgota yayi ya sake juyo da ita yace"bana son raini wlh gaya min wa ya dake ki nace!ko kuma iskancin da kike min ne suma malamman kika je kina musu,kut!zaki daina bokon nn ne wlh tunda ba kya ji,tayi saurin kallon shi le6ace da baki zuwa kuka tace"wlh Aa shine yake takurani kullum wae shi a dole sae naje office d'insa..... What! kije office d'insa fa! tace"eh wlh hk kullum yake aikowa ni kuma bana zuwa shine yau yaje har class d'in mu ya same ni yana gaya min wae shi sona yake shine na mai tsawa nace ya fita haraka ta ni ba irin en matan nn bace shine kawai ya sami bulala ya daken" Cikin mugun 6acin rai ya damqota kafad'unta yana kallon fuskarta yace"kinga bana son qarya fa!meye abin so a tare dake da zai wani nace miki! kawai dai kin mae iskanci kmr yanda kike min ko! Tace"wlh gobe ma kaje ka tambayi en class d'inmu kaji" Ya nunata da yatsa snn yace"idan na samu laifin ki ne fa" Tace"kawai ka cire ni daga bokon" yace"yayi kyau Allah kaimu goben" Nn ya tafi awa zai tashi sama ita kuma ta rufe bathroom d'in ta watsa ruwa ta fito tayi sallar zuhur. Washe gari Friday tun safe yazo d'akin Rynt yace da ita"mami kad'ai zaki yi ma shirin school bada ke ba"kmr zatayi kuka tace"meyasa? yace"sae na gama bincikena tukun" Ajiyar zuciya ta sauke tace"to" Har zai fita sae kuma ya juyo yace"ya sunan malamin? Tace" malam a shaqata.... bana son raini sunan sa na qwarai zaki gaya min,to ni ban sani ba ai da haka kawai nake jin ana kiranshi, Tsaki kawai yayi tare da fita d'akin yana fad'in"zai shaqata a cell don ubanshi" 4:05pm Rynt ce zaune ta gama sallah wacce tun sha biyu da mami ta dawo school take jiran shigowar man amma taji shiru sae roqon Allah take kar malamin ya lauye ta bokon ta ko ya sami matsala tana cikin hakane sae ga man ya fad'o d'akin yaje kan bed ya zauna ya tasa ta gaba yana kallo sae can ya girgiza kai yace"kin rainani ko?a rikice tace"me yace maka ne wlh ko mene ne qarya ya maka" Yace"kinga yi min shiru! Dan ubanki ashe ba kya saka niqabi cirewa kike idan kinje school! A d'an daburce tace"ni kuma" Yace"akwai wata ne banda ke to bari kiji bake ba bokon nn kuma wlh ba inna ba ko Abba zaki kai qarata agunshi baza kiyi nasara ba kuma ki gwada ki gani shege ka fasa! Nn ya tashi zai fita ta tashi da hanzari tasha gaban shi inda cikin marairaicewa tace"kayi hqr dan Allah" Tsaki yayi ya tureta ya wuce wanda har yakai bakin qofa ya mird'a handle tasha gaban shi tare da riqe handle d'in tace"kar ka fita dan Allah kabari nama bayani" Yace"wane bayani kin tallata fuskar ki kuma kin samu an yaba sae kuma me! Tace"bafa haka bane wlh en makarantar ne suka takurani suna ta magana akai shine na cire" Gud idea kin kyauta ma kanki. Oya!bani hanya na wuce! Tace"nidai don Allah kayi haquri ka barni na ci gaba da boko na" Yace"kije su da suka saki daina sa niqab d'in su maida ke makarantar very stupid! Nn ya mird'a handle zai fita tasa hannunta duka biyu ta riqe tana roqon yayi haquri, A fusace ya d'aga hannu zai mareta tayi saurin sake handle d'in ta kare fuskarta cike da tsoro had'e da fashewa da kuka tana bashi hqr,bai marenta ba sae ture ta yayi daga jikin qofa ya bud'e qofar ya fita. Haka Rynt tayi weekend cike da damuwa ganin bakin rai bata zuwa school mami kad'ai ake kaiwa haka ma lesson ana gama ma mami lesson teacher ke tafiya . Rnr lahadi da qarfe hud'u tana jin mae lesson yazo ta had"a komai nata na lesson taje tayi zaune falo ta fake yana gama ma mami tazo zata zauna ya kwashi kayansa yace"kiyi hqr yace qaramar nn kawai za'a ci gaba da yi ma lesson " gyad'a mae kai tayi tana mai danne hawayenda ke qoqorin zo mata. Zata haura sama kenan taji fitowar man yana magana a waya taje gurin sa ta tsaya tare da sadda kanta qasa yana gama wyr yace lafiyar kin wani zo kimmin tsaye ,hawayen idonta kmr zasu zubo take kallon shi tace"don Allah kayi haquri ka barni naci gaba da karatuna kaji" Kallon ta kawai yayi yace"naji amma je ki gyara min d'akina" Da sauri ta fiddo ido waje tace"cab! Allah sauwaqe wlh bazan sake gyara ma d'aki ba" Ya kalleta da kyau yace"ke me kike nufi ne to idan har ma wnn abun kike tunani ki cire dmn sanin kanki ne qaddara ce ta afka min a wnn rnr ina kuma roqon Allah da kar ya sake had'a ni da irin wnn qaddarar,cikin 6acin rai mai had'e da muryar kuka tace"ai dole kace haka tunda ka gama cutar dani,mugu kawai wlh bazan barka ba! Nn ta fashe da kuka ta tafi da gudu tabar shi nn tsaye cike da mamakin yanda renin wayonta ke qaruwa a kanshi,sae jin yayi malika ta rungume shi ta baya tare da fad'in "my man albishirinka" ya kalleta d'ai ,ita kuma ta rad'a mai magana a kunne da tasa shi wani irin matsanancin farin ciki kai tsaye , ya ta6o cikinta yace"dagske malika! tace"wlh kuwa my man muje ma ka duba a PT strip" Nn yaja hannunta cike da farin ciki suka tafi d'akin shi. Bayan sllr isha'i Rynt ta gama sallah d'auke da hawaye a fuskarta tana tunanin hanyar da zata bi ta samu taci gaba da bokon nn don dai kam koda kuskure bata son ta sake zuwa d'akin man bare har yayi galabar sake cutar da ita. Tana cikin hkne taji qarar bud'e gate ta tashi a hnkli ta yaye labulen windonta ta hango motar man ce ta fita ta saki labulen tana mae tunanin idan har zai barta ta koma school in ta gyara mae d'aki ,gwanda kawai tayi sauri taje ta gyra mae kafin ya dawo nn ta kalli mami dake kallon tom and jerry tace"mami muje ki rakani a d'akin yayanki sae ki kunna kallon ki a can kinji" Ba musu mami ta tashi suka je Rynt ta gyare koina tsaf cikin en mintinan da basu fi 30 ba wacce har ta gama gyara d'akin gabanta na dukan uku uku. Tana gamawa taja mami suka koma d'aki. Sae bayan awa 1 da komawar su d'aki ne taji qarar bud'e gate ta tashi ta duba taga motar man ce ta kunno kai. Byn an parker motar driver ya fito da sauri yaje ganbun baya ya bud'e ya kuma zagaya da sauri ya bud'e d'ayan,nn man da malika suka fito kowannen su d'auke da fara'a a fuskar shi man ya riqa hannun malika suka shiga gida yayinda driver ya bisu da kaya niqi niqi. Rynt ta saki labulen ta koma ta zauna. Har sha d'aya na dare Rynt batayi bacci ba sbd jiran ko man zai shigo idan yaga ta gyara mae d'aki amma shiru kmr shirwa ta cinye d'an tsako. Gashi sosai take jin bacci amma tasan ko ta kwanta bazata iya yinsa ba idan ba taji, ko zai barta ta koma school ba. Har sha biyu shiru bai zo ba, gata kwance amma fir bacci yaqi d'aukarta sae juyi take, ta kalli gefen mami da tuni tayi bacci abinta ,ta tashi zaune tare da had'e kai da guiwa sae jin tayi an bud'e qofa tayi saurin d'ago kanta yayinda hawaye ke silalowa a hnkli kan kumatun ta. Man ne ya shigo yayi tsaye a bakin qofa yana kallonta ita kuwa sau d'aya ta kalle shi ta kauda fuska tare da share hawayenda suka zubo mata ya qarasa cikin d'akin yaje kan bedside drawern da ke kusa da Rynt ya zauna snn ya kalleta ba yabo ba fallasa yace"lafiyarki kike kuka da daren nn" Tace"kace idan na gyara ma d'aki zaka barni na koma school ko"yace"yaushe nayi dake haka? kmr zata yi kuka tace "d'azun kmr hk fa ka nuna min" A tunanin ki kenan amma ni ba hk bane,ya fad'i hkne tare da kallon fuskarta sae yaga nn take hawaye sun zubo mata nn yaji ta burge shi sosai sbd yanda take son karatu. ya sauke numfashi snn yace"zan barki ki koma d'in amma fa da sharad'i"da sauri ta kalle shi tace"ina jinka gaya min" Yace"Duk kika bar wani malami ya sake fad'awa sonki ko wlh bake ba makarantar koma nace gabad'aya bokon don ba kud'in banza nake dashi da zan kai ki karatu kije kina soyayya ba idan kuma har kince soyayya zakiyi ni kinma hutar dani kuma kin hutar da kud'ina don sallamar ki zanyi ki koma can gidan inna da taji zata iya. Rynt ta sauke ajiyar zuciya tace" naji zan kiyaye,yace"idan ma kin kasa kiyayewa wa kanki, Nn ya fita tayi hamdala wa ubangiji ta kashe wutar d'akin ta kwanta. Washe gari da taje school wata qawar ta da suke shiri sosai take ce mata "bari Rynt yanyanki yayi wlh don naji dad'in da yasa aka kori malam a shaqata daga mkrntr nn shikenan yanzu mun huta da muguntar shi" Rynt tace"hm korar sa yasa akayi?au bai gaya miki bane? tace"um um" Hm bari kedai naso ace rnr Friday d'in nn kinzo wlh don qaramin yaqi aka tashi yi a makarantar nn dmn en sanda fa yayanki ya kiro mishi yace a tafi dashi sae da qyar principal ta shawo kan yayanki a cewar yayi hqr kar yasa a kama shi zata sa ayi mai transfer zuwa mkrntr maza don dama ta jima da jin wasu halayen shi maras kyau da ake fad'i. Rynt ta kalli qawar ta tace"to a bakin wa yaji cewa bana sa niqab hln?tace"gsky ban sani ba kawai dai munji hayaniyar fad'an su ne" Qawar tace"amma yayanki yayi aure ko? Rynt tace"eh" tace"kai amma fa ko waye matarsa tayi sa'ar miji kuma kema kinyi sa'ar yaya" Ta6e baki kawai Rynt tayi ta jawo littafinta tana dubawa sbd haka take ko yaushe ko ba test idan dai basa komai a aji ,bazatyi strn banza ba sae dai ta jawo littanfanta tana karatu. 5:00pm Rynt ce da mami sun dawo daga school suka sami malika da mohd zaune a falo ,malika nata zubawa man kukan shwaga6a wae ita yunwa takeje bata iya cin abincin kuku don ko warinsa bata son ji. Tana ganin su Rynt sun shigo tace"yauwa my man kasa wnn abar ta dafa min abinci wata qil ko zan iya cin nata. Rynt na jinta taji sa6o ma take bata dai kula su ba tayi ficewar ta ita da mami. Shi kuwa mohd kmr ma ince tare suka shigo d'akin shida su Rynt , Ya kalli rynt dake qoqarin ajiye school bag yace "ke yi sauri ki cire uniform kije ki d'aurawa malika abinci" Rynt ta ta6e baki tace"hm wae sa6o idan bazata d'aurawa kanta ba ai sae ta zauna da yunwar" Yace"bana son raini wlh maxa ki cire uniform kije ki d'aura mata girki " Tace"wae ya zaka ce na d'aura mata girki wane irin ma rashin tausayine ynx daga dawowata daga mkrnta" Yace"haka zaki ce to bari kiji idan har kina son ci gaban karatunki to fa lallai sae kinyi abinda nake so wlh" Tace"naji amma bafa zan d'aurawa qatuwar banza girki ba" Yace"well ya rage naki idan kina son ci gaban karatun ki kije ki d'aura mata girkin idan kuma ba kya so ba dole sae kiyi zamanki. Billy Giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [10:24PM, 2/2/2017] Billy giro😊: [2/2/2017] ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮``` 🔮🔮🔮🔮 *page* *```42```* Yana gama fad'ar hk ya fita. Wani irin baqin ciki ne ya tokare Rynt a wuya da har ta sami kanta dajin qwalla sun cika mata ida bata dae bar sun zubo ba ta ajiye school bag ta cire takalmi da socks takai su inda ya dace snn ta fito downstairs ta wuce su man zaune a falo ta tafi kitchen ba tare da tako kalli gefen su ba. Malika tace"matsiyaciya ai da na d'auka ko bazata fito ba" Man yace"dolenta mana tunda tana son ci gaban karatun ta. malika ta tashi tare da fad'in "bari ma naje naga wane d'an iskan abinci ne take da niyyar dafa min. Rynt kuwa tana shiga kitchen ba abinda tayi niyyar dafawa sae indomie har ta d'aura c pot ta zuba ruwa sae ga malika ta shigo ta kalli Rynt a yatsine tace"ke matsiyaciya me kike shirin dafa min ne "Rynt tayi banza da ita ,malika tace"idan kin iya kar ki bani amsa amma wlh ina mae gaya miki kar ki kuskura ki dafa taliya ko indomie,sakwara zaki min da miyar agusi" Still dae Rynt bata tanka ta ba har ta fita taje gurin man cikin masifa tace"wae da yrnyr indomie na samu zata dafa min don ta rainani" Yace"wae da to me kike son ta dafa miki? Sakwara mana da miyar agusi,ya kalleta yace"amma kinsan tana da lesson 5:30 to six har yaushe ta gama,da dai kin barta kawai ta dafa miki indomie d'in, kallon sa tayi tace"ban gane ba tausayinta kake ji ne ko yaya? Yace"ko d'aya mae lesson d'in ne bana son ta 6atawa lokaci" Tace"to ai sae a farawa mami idan ta gama min girkina sae a mata" Yace"ok" Suna nn zaune cikin en mintina sae ga Rynt ta fito riqe da plate d'in indomie takai kan center table d'inda ke kusa da su ta ajiye ta kuma yi ficewarta. malika ta bita da ido sake da baki snn ta kalli man da ya gama waya knn tace"kaga er iska indomie d'in fa ta dafa min" Ya tashi tare da fad'in "bari ina zuwa" Yaje ya sami Rynt tana shirin shiga bathroom tayiwa mami wanka , ya dakatar da ita cikin cewa"ke zo nn "bata je ba sae kallon sa da tayi yace"me malikà tace miki ki dafa mata? tace"sanin kanka ne ban iya wnn abincin ba don ni abu biyu kawai na iya dafawa daga taliya sae iñdomie....bana son raini da kike dafawa a gidàn inna fa? Tace"Bani ba kam sae dai ko baba hurera" kallonta yayi kmr zai ce wani abu sae kuma ya fasa ya fita, Rynt ta ta6e baki ta bishi da ido wacce ba klr abincinda bata iya ba a gidan inna qin yine kawai tayi. Taja hannun mami dake fad'in"wae anti meyasa anti amarya yau tace bata cin abincin kuku? Rynt tace" oho mata kedai muje ayi wanka muci abinci kafin mae lesson yazo ko" Mami tayi murmushi dan da murmushi Rynt tayi mata mgnr, wa enda tuni sun shigo bathroom sae ruwa Rynt ta had'a tayiwa mami wanka byn ta gama mata mami ta fita ita kuma tayi nata. Mohd kuwa koda yaje ya snr da malika cewa Rynt bata iya wnn abincin da tasa ta ba sae masifa take ita lallai sae Rynt tazo kuku ya nuna mata yanda ake don ita kam baza taci indomie ba da qyar man ya samu ya lalla6ata har ta yarda taci indomie a cewar gobe sae Rynt ta dafa mata duk abinda take so. Rynt tana fitowa wanka sharp sharp ta shirya suka ci abinci sae dai koda suka gama har sun shigo cikin lokacin lesson d'inta tayi saurin kwasar littafanta ta tafi ta samu kuwa har mai lesson d'in yazo yana jiranta. Wnn karon man baizo ya fake kmr ko yaushe ba don yana can shida malikarsa a d'aki. 6:00 ake gama mata lesson d'in sae ya farawa mami ana yin magrib ake gama mata ita kuma. But rnr Thursday ,Friday Saturday and Sunday suna samun enuf time da ake yi musu lesson bcs thursday 2:00 ake tashi friday 12:00 then asabar da lahadi islamiya ce 8am suke zuwa su dawo after 2 yayinda duk ranakun nn hud'u da qarfe hud'u lesson tearcher d'in ke zowa bashi yake barin gidan ba sae anyi magrib. Bayan 2 dayz duk kwanan nn biyu Rynt ke dafawa malika abinci idan sun dawo daga school amma ba wani abinci bane face indomie wacce take silalawa sama sama takai ba tare da ta damu da ta nina ko bata nina ba. Gashi kullum malika sae masifa take yiwa man ita tgji da cin indomie a kira kuku ya nunawa Rynt kallolin abinci ta riqa dafa mata,Man kuwa sae rarrashinta yake yana lala6ata sbd hk kawai yaji baya son kuku ya koyawa Rynt abinci inda dae mace ce. Rnr dai ta matsa mai kan dole ya kira kuku suka sami Rynt a kitchen ,man ya dakatar da Rynt dake shirin d'aura indomie snn yace da malika"me kike son ta dafa miki ? Nn ta shiga shafa cikinta a yangace snn tace"inaga yau jellop rice muke ra'ayi nida babynka amma taji busasshen kifi da manja a kuma zuba ganyen alanyafu snn ayita da yaji sosai" Yace"shikenan abinda kk so? Tace"eh ni zanje na kwanta na huta nagaji da tsayuwar nn yace"ok"snn ta fita nn ya maida dubansa gun Rynt yace"oya ga kuku nn zai nuna miki komai yanda zakiyi". Kallon sa kawai tayi snn ta kalli kuku shi kuma man ya nemi kujera ya zauna yana duba jarida. Kuku yazo gaban Rynt ya had'a komai da za'a sa a jellof d'in snn ya d'ura c pot ya zuba manja a cewar idan ya d'auko zafi sae ta saka niqaqqin tattasai da albasa da tarugunda aka niqa sama sama bayan en yankakkin da ke ajiye gefe da sae jellop d'in ta d'auko dafuwa xa'a saka su. Hanklin kuku nakan busasshen kifin da yake d'an qara gyrawa yayinda Rynt ke kallon manja har yayi mugun zafi ,ta d'auko kofin ruwa kai tsaye ta kwara cikin manjan, baaa! belar wuta ta fito tayi sama! ai kuwa Rynt ta buga ihu da ita har kuku ba mae kama wani sae qoqarin 6ira suke su fad'i wanda tsirif ya rage Rynt ta fad'a kan jikin kuku man yayi saurin tashi ya fizgota zuwa jikin shi, Yayinda cikin mugun 6acin rae man ya kalli rynt yace"u are very stupid! ke ba kya ganin inda zaki fad'a ne! Ta rufe ido gam had'e da fashe mai da kuka wacce da gayya ta zuba ruwan amma tayi mugun tsorata da ganin yanda wutar ta fito a manja, dan ynz hk jikinta sae qyarma yake. Man kuwa ganin yanda Rynt ta rufe idanunta sosai tana kuka ,ya d'auka ko manja ya shiga mata a ido nn yakai hannu zai bud'e ya hura mata idon amma taqi yarda sae tsalle take tana kuka bayan ba abinda ya shiga mata a idon pretending ne kawai don ta samu ta zillewa girkin. Da hk ta qirqiro tari tana tayi se duk Man ya damu ya rasa yanda zai mata ya kalli kuku cikin daka mae tsawa yace"dan Allah qaton banza tashi kaje ka kashe wancan abun duk yabi ya damu mutane! Da hnzari kuku ya tashi yaje ya kashe gas cooker, man kuwa yaja Rynt har zuwa d'akinta wacce sae tari take ga kuma idanuwanta dake rufe still . Bathroom ya nufa da ita ya wanke mata fuska ya ciro farin handkerchief d'insa ya share mata fuska snn ya fito da ita ya zaunar kan bed tana d'an ci gaba da tari kad'an kad'an nn yaje ya tsiyayo ruwa a glass cup ya zauna snn yace"bud'e idonki ga ruwa kisha " Qin bud'e idon tayi sae hannu takai tana lalube sae jin tayi yakai cup d'in ruwa a bakinta tasha ruwan kad'an ta kwanta shi kuma yasa blanket ya rufa mata jikinta ya fita sae a snn Rynt ta bud'e idonta a hnkli tare da saurin yaye blanket ta tashi ta watsa da gudu bathroom sbd fitsarin da yayi mugun matsar ta. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [9:54AM, 2/4/2017] Billy giro😊: [2/4/2017] ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮``` 🔮🔮🔮🔮 *page* *```43```* Mohd kuwa d'akin malika ya nufa ya sameta kwance kan bed sae chat take tana qyalqyatar dry. Ya zauna kusa da ita ta mirgino tayi pillow da cinyoyinshi tana ci gaba da chat d'inta,ya kar6i wyr yace"wnn yrnyr fa in banda shirme ba abinda ta iya kawai kiyi hqr na nemo wata yrnyr da zàta riqà mana girki shi kuma kuku ya kama gabansa don ynz sam bana son ina ganin sa a gidan nn, da hanzari ta tashi zaune tare da fad'in"ban gane ba nifa gsky wnn abar nake son ta riqa min abinci don ma ka daina zancen d'auko wata kuma kuku meye mtslr shi, shida ma zai riqa koya mata kalolin girki. Malika na gaya miki bazata iyaba don in banda shirme da qoqarin qona min gida ba abinda ta iya . Tace"wae kamar ya ban gane ba? Yace"baza ki gane bane tunda ba'a a gaban ki ta tafka shirmen ba. Tace"to ai koma yaya ne yau da gobe zata iya" Mtsw mohd yayi d'an guntun tsaki yace"malika bana son gardama kin sani, ki bari kawai a nemo maki wata yrny ba dole sae ita ba" Cikin fushi ta sauka kan gadon tace"wlh gsky ni ita zata ci gaba da girka min abinci idan ba hk ba kuwa wlh sae dai a zubar da cikin nn kowa ma ya huta" Kmr saukar guduma yaji zancen ya sauka a kunnen shi ya tashi da hanzarinsa ya qarasa gurinta ya riqo kafad'unta cikin mugun damuwa yana kallon fuskar ta yace"malika kinsan me kike fad'a kuwa ,a zubar da cikin nn fa kika ce" Kuka ta fashe dashi snn tace"eh mana ina son cikin nn amma dole zan zubar dashi tunda baka iya d'aukar lalura ta da duk wani abu da nake so" Rungume ta yayi yace"is ok naji zata ci gaba da yi miki girkin amma sae abinda ta iya zata girka miki kin yarda" Ya fad'i hkne yayinda ya d'ago fuskarta yana kallonta ,ta share hawayen funafurcin dake kan fuskarta tace"to ya zanyi my man tunda babynka ya d'aura min lalurar son cin abincinta,amma kuma gsky yau bazan ci indomie ba sae dai ko fita zamuyi a siyo min gasasshiyar kaza na d'aura da hollandia milk" Yace "to ai wnn mae sauqi ne shirya muje" Tace"ai a shirye nake mayafi kawai zan d'auko nn taje ta ciro mayafi ta yafa suka fita. 9:00pm Rynt ce kwance cikin tunanin anya ko za'a maida mami kuwa sbd yau suna dawowa school abinci kawae suka ci aka kai mami gida. Tana cikin hkne taji qarar bud'e qofa tayi saurin kallon qofar don a tunaninta ko mami ce sae taga man. A bakin qofa ya tsaya yana tmbyrta mami fa? tace"ka manta tana gida" Agogon hannusa kawai ya kalla ya juya zai fita Rynt tayi saurin katse shi da cewa"don Allah idan d'auko ta zakaje zan bika" wani kallon kin raina ni ya mata snn yace"me zakije yi a gidan ?tace"zan gaida su mama ne na jima banje ba wlh" Yace"shikenan ki same ni a waje idan kuma kin jima zaki samu bana nn" Yana fita tayi saurin zuwa ga wardrobe ta bud'e ta nemo wata doguwar rgr atamfa ta cire riga da wandon baccin da ke jikinta ta saka ta nemo hjb ta fesa turare tasa snn ta d'auko takalmi tasa ta fita da sauri har tana hard'e qafafuwa. Koda taje har ta samu ya tada motar shiga kawae tayi yaja suka tafi. Suna isa gidan 6anfaren su mohd suka fara nufa ,ummar sa suka samu zaune a falo sukayi sallama sae kallon su tayi ba tare da ta amsa ba,har qasa Rynt ta durqusa tana gaida umar tashi wacce ta watsa mata muguwar harara Rynt ta tashi abinta zasu bar 6angaren da ita hr man da shima ya gaida ummar tashi bata amsa ba. Lokacin da suke qoqarin fita ne Abba ya sauko nn downstairs Rynt na ganin shi tayi saurin durqusawa tana gaida shi, ya amsa da fara'ar sa yana fad'in"yau kune a gidan " Tace"eh Abba" Yace "to ya gida ya karatu tace"duk Alhmdlh" Byn nn ne man ya gaisa da Abbanshi snn yace"mu zamu tafi Abba dama mami ce muka xo d'auka " Nn Abba ya ciro 5k a aljihu ya bama Rynt wacce taqi kar6a har sae da qyar Abba ya samu ta kar6i kud'in tayi mai godiya snn suka fita. Tare suka je 6angaren su saliha mami na ganin su tazo da gudu ta riqo hannun kowanen su. Umman mami har Abbanta duk suna nn zaune a falo nn su Rynt suka gaida su man ya fita a cewar yana jiran su a waje,da yake mami a shirye take sae bin yayan nata tayi, hkn yasa itama Rynt ta tafi zata bisu umma ta kirata suka tafi d'aki. Turarukka ne masu qamshi umma ta bata da kuma kayan kwalliya wad'anda dama a tsare suke cikin ledar su da aka yo shopping tayi niyyar bawa mami ne ta kai mata sae gashj taxo. Rynt ta kar6i ledar tana yiwa umma godiya,,umma tace"ai inshaAllh kwanakin zan zo gidan naku"tace"to mama sae kinxo" Har Rynt zata fita umma tace"af na manta fa rnr da mukaje visiting akwai wani saqo da saliha ta bani tace na baki har ma tace tana gaida ke,Rynt tace"Allah sarki mama bata ce dake fushi take dani ba? um um ko d'aya kawai dai ta shiga damuwa sosai dajin kinso zowa mohd ya hana,Rynt tace"hln inna ce ta gaya mata ko" Mama tace"eh kam don inna sae fad'a take tayi ganin har za'a tashi visiting baki zo ba,don tace mana har zaku shiga mota mohd ya same ku yace mata su su tafi wae zai kaiki daga baya" Rynt tace"Hm hk yace mata mama" Mama tace"to ko meyasa yayi hkn kuma sae bae kaiki d'in ba, koda yake hln mohd sae shi. ta fad'i hkne tare da d'auko wata er qaramar leda tace"kinga saqon amma kuma ban san ya akayi ledar ta yage ba, bari na cire nasa maki a cikin ledar kynki. Nn mama ta ciro kayan ta saka a cikin ledar turarukka da kyn kwalliyar da taba Rynt,Rynt tayi godiya tafita tana sauri don tasan man ya gama suqewa da jiranta. koda tazo sae fira ma ta samu sunayi shida mami a cikin mota. Tana shiga ya tashi motar suka wuce. A maimakon yaje dasu gida sae wani babban mall ya tafi dasu. Shida mami kawai suka shiga suka bar Rynt cikin mota. Chocolate, biscuit,sweet n drinks ne suka siyo wato kayan mami da ake d'ibar mata tana zuwa school dasu. Bayan su basu riqo komai ba sae ice cream . Tun a mota mami ke shan ice cream d'inta wacce koda suka iso gida ta shanye har tayi bacci. Da suka iso gida man ne ya d'auki mami da tayi bacci, Rynt kuwa kyn hannunta kawai ta d'auka ta shiga cikin gida shi kuma man kuku ne yazo yana jidar kyn da suka siyo yana shigar dasu. Rynt da shigarta d'aki ta d'auki kyn baccinta ta nufi bathroom ta saka ta fito linke da wad'an da ta cire taje ta saka a wardrobe taje ta kwanta sbd wani irin bacci da take ji . Sae a snn man ya shigo ya shinfid'e mami yaje ya shigo da kayayyakin da suka siyo. Yakai ledar ice cream kan bedside drawer ya ajiyewa Rynt nn idonsa ya qyalla kan ledar Rynt dake ajiye a gun. Har zai wuce sae kuma ya tsaya yana kallon farin abinda yake hangowa ciki, kai tsaye yakai hannu ya ciro kyakkawar sabuwar farar bra da kuma farin pant,ya cira kyn sama yana kallo yayinda Rynt ta rufe idonta cikin mugun jin kunya wacce kwata kwata bata lura da sune mamar saliha tasa a ciki ba duk a tunaninta farar vest ce saliha ta siyo ta aiko mata. mohd ya ajiye kyn snn ya kalli Rynt da taqi yarda ta bud'e idonta yace"dama don kije ki roqo wasu kayan ne yasa kika bini" Bata bud'e idon ba sae cewa tayi"Allah sauwaqe ni wlh roqo ba halina bane" Yace"ok idan har baki akayi to meyasa kika kar6o byn duk tulin irin kyn nn da kk da su a cikin akwatinanki ko kuma kina nufin kaf kin murje su" Komai qin ce masa tayi hkn yasa ya tafi sae gurin akwatinan ta ya bud'e wacce undies ke ciki , komai na ciki ba abinda tayi aiki dashi sae qwarorin vest da pant amma kuma se duk baiga bras ba sae wata babbar farar leda ya gani da qunshin kayanda bai san meye a ciki ba, bud'e ledar yayi ya zazzage kaf abinda ke ciki ga mamakinsa sae yaga duk brasseries d'in ne ba wacce aka ta6a, nn yaje ya jawo Rynt yazo da ita gurin akwatinan ya nuna brassieres d'in yace"uban wa kk son ya saka wad'an nn kyn da har yazun ba alamar ansa ko d'aya! Komai bata ce masa ba asalima ko gefen akwatinn taqi yarda ta kalla sbd bra na d'aya daga cikin abinda Rynt tafi kunyar gani sosai. Mohd kuwa tsawa ya daka mata yace "wae bada ke nake magana bane! Kmr zatayi kuka ta kalle sa tace"to ai ni ban fara sawa ba nayi qanqanta" Qirjin ta ya kalla tare da fad'in"what!sae kuma yayi tsaki yace"kaji mtslr bagidajen mutum kuda kanku ke 6atawa kanku tsari snn ya kalleta tare da fad'in" to wlh bari kiji by tomorrow ki tabbatar kin fara sakawa idan kuma kika qi nida da kaina zan saka miki, kuma kiqi d'in kiga ikon Allah. Daga hk ya fita yabar d'akin , Yayinda Rynt tayi saurin rufe akwatin undies tana qunquni ita wlh bazata sa wnn abin kunyar ba. Taje ta d'auki wad'anda saliha ta aiko mata har ta ware ta kalla sae kuma tayi saurin rufe idonta ta dunqule taje ta tura cikin akwatin undies. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [10:33PM, 2/4/2017] Billy giro😊: [ 2/4/2017] ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮``` 🔮🔮🔮🔮 *page* *```44```* Washe gari da safe Rynt ce ta fito daga wanka d'aure da towel sae sauri take zata d'auko hjb a wardrobe sbd wanda ta shiga dashi wanka tayi rashin sa'a garin d'aukowa ya fad'i ya jiqe se ma ta wanke shi gabad'aya. Kafin takai gun wardrobe sae ga man ya fad'o d'akin tayi saurin komawa bathroom tana fad'in wae meye hk dan Allah sae ka shigowa mutane d'aki ba sallama. Qala bae ce da ita ba sae time ya kalla snn ya kalli mami dake kwance tana sharar bacci. Yace da Rynt"fito ki tashi yrnyr nn ki mata wanka lokaci ya tafi" Tace"to kafita mana" Yace"gaya min abinda zaki d'auko na kawo maki" Tace"hijabi nake so yana cikin wardrobe" Nn ya tashi a maimakon yaje wardrobe sae ya nufi gurin akwatinan ta ya bud'e akwatin undies ya ciro bra da pant d'inda saliha ta aiko mata yaje dasu har bakin qofar bathroom yace"kar6i" Ta bud'e qofa kad'an ta turo hannunta ya d'aura mata bra da pant,tayi saurin jefar dasu tace" wae meye hk dan Allah nifa hjb nace" Ya d'auko kyn tare da fad'in ki fara saka wad'an nn tukun, tace" wlh bazan sa wnn abir kunyar ba, Yace"gud baki tashi fitowa ba knn" Tace"Aa dan Allah kar kasa muyi letti" Baice da ita komai ba sae mami yaje ya tayar yaje da ita qofar bathroom yace"bud'e ga mami ki mata wanka" Kad'an ta bud'e qofa ta leqo ta hango mami tsaye snn ta d'an qara bud'e qofar ,mami ta shiga ta rufe. Bai fita ba yayi zaman sa har ta gama ma mami wanka da zata turo mami ta hango shi kwance abinshi kan bed yayi pillow da hannyensa ya kuma d'aura qafa kan qafa yayinda idanuwansa ke rufe wanda ga dukkan alama ya soma yin bacci. nn ta rad'awa mami magana a kunne tace"idan kinje ki d'auko min hjb amma kar ki bari yayanki yaji motsin ki " tace"to Anti" Taje a hnkli a hnkli ta bud'e wardrobe sannu, ta hango hijabban Rynt duk sama suke bata cimma ko d'aya, daga nn inda take ta bud'e murya tace"Anti gurin hijabbayanki ya min nisa" Firfigit man ya farka daga d'an guntun baccin da ya d'auke shi wanda kai tsaye idonsa ya fad'a gun Rynt dake la6e a bayan qofar bathroom ta fiddo kanta yatsanta akan lips d'inta tana fad'in mami tayi shiru. Tashi zaune yayi tare da watsa mata mugun kallo ta rufe qofa da qarfi cikin jin haushi mai had'e da son tayi kuka. Man ya kalli mami wacce ke fad'in "yauwa yaya ka tashi? anti ke son a d'auko mata hijabi zaka d'auko mata? Ya lumshe ido a hnkl ya kuma ware su snn yace"je d'auko Vaseline ki shafa tukun " Nn ta nufi dressing mirror shi kuma ya tashi ya ciro mata uniform a wardrobe d'inta. Byn ta shafa Vaseline ya bata uniform ta saka tare da taimakon shi,snn yace"taje ta kar6o break fast a gurin kuku mami na fita Rynt na bud'e bathroom da sauri dan ta d'auka ko man ne ya fita. Ido hud'u sukayi ita da man yayinda ta marairaice mae fuska kmr zatayi kuka yace"Allah ina gaya miki idan ba kin saka wnn bra ba ko, ba inda zaki" Cikin murya kuka ta rufe bathroom d'in tana fad'in "wlh bazan saba uhm uhm" Bai sake ce mata komai ba har mami ta dawo d'auke da plate biyu tace"har da anti na kar6owa" yace"to ci naki idan ta fito sae taci nata" Tace"to yaya anti zata sa muyi letti fa kabata hjb ta fito" Yace"ai ke bazakiyi letti ba kina gamawa za'a kaiki" Tace"ita anti fa? Yace"ita ma idan ta shirya za'a kaita" Daga nn mami tayi shirunta tayi breakfast d'inta tana gamawa ta d'auki koman ta na zuwa school har dasu chocolates,biscuit da drink, Mohd yace"idan kin kar6i lunch box d'inki a gun kuku sae kije driver ya kaiki kinji" Tace"to yaya amma pls ka d'aukowa anti hjb tayi sauri ta shirya kar tayi letti a mata bulala" Yace"naji" Nn ta fita shi kuma ya tashi ya d'auki bra yaje jikin qofar bathroom yace"oya bud'e ga hijab d'in" Ba musu Rynt ta bud'e tare da turo hannunta sae jin tayi yaja hannun ya fito da ita a toilet corner ta fasa ihu tana qoqarin komawa bathroom ya fizgota ya kama duk hannuwanta ya maida baya ya riqe da d'ayan hannun sa snn ya manna ta a jikin bangon toilet corner d'in. Kuka ta soma yimae yace"shiiii bana son jin kukanki,meyasa ke mutum baya binki da lalama ne? Dake nake ki gaya min! To ni bazan iya sawa bane don Allah ka rabu dani, yace"ke ko kunya ba kya ji duk wnn ubañ qirjin naki kice ba kya saka bra sbd gidadanci irin naki ko ,bari kiji ni taimaka miki ne zanyi don idan baki fara sa bra a yanzu ba nn gaba zasu dawo miki ne tmkr ledar pure water" Turo baki tayi tace"ba wani nn kuma ni Allah tsare ni wlh can da bakinka" Tsawa ya daka mata har sae da ta tsorata yace"dan ubanki meyasa kika raina ni wae!gaya min meyasa! A rud'e ta qara manna jikinta a bango. Ya sake daka mata tsawa yace "wlh idan baki gaya min ba zan rabaki da towel d'in nn na kuma zaneki! Gama fad'ar hk yakai hannu zai fizge mata towel, Ta fasa ihu a rikice tace"wayyo Allah zan fad'a" Yace"oya inajinki gaya min" Sae da ta turo baki snn tace"to ai duk kaine ka siya abinka" Da mamaki yace"ni d'in da kaina lallai ma yryr nn keda at all bansan ko ke er gidan uban waye ba daga kawai ina ganin ki gidan inna shine kika wani rainani,ko kuma gani na da kike ya kawo rainin! Tace _"kashe min mahaifi dae dakayi kuma wlh bazan barka ba"_ tayi mgnr ne a rai yayinda a fili ta fashe da kuka snn tace "nidae kayi hqr ka barni na tafi school dan Allah" Yace"ai school ke kika hana kanki zuwa" Tace"wae don Allah meyasa kake son takura ni ne wlh ni bazan iya sa wnn abar ba" Yace"ai ni zan iya sa miki d'in" Tayi saurin cewa "nifa ba hk nake nufi ba"Yace"ai kinsan na gaya miki duk baki saba da kaina zan sa miki" Tace"wlh bana so" Bai kula ta ba sae hannuwanta da yake riqe dasu ya sake yana qoqarin sakà matà bra, tayi sauri zata kwasa aguje ya damqo towel d'inta ai kuwa ya rabu da jikinta ta fasa ihu ta koma bayan shi da gudu ta 6uya tana fad'in"don Allah kar ka juyo kayi hqr kaban towel d'ina" Sosai abin ya soma ba man dariya don gabad'aya ta daddamqe shi sae roqon take kar ya juyo danne dryr da yake ji yayi yace"meye kuma ban gani ba bayan a gaban idona towel d'in ya zame" Tace"ba abinda ka gani wlh" kai tsaye taji ya jawota ya mannata a qirjin shi yace"wae bakin ki baya mutuwa ne ke kam" Bata iya ce masa komai ba sae qoqarin komawa bayansa take ta 6uya yayinda shi kuma yake qara mannata a qirjinsa,yace "wae meye abin 6oyo a jikin naki ne keda kan qwailancin ki bra ma baki fara sakawa ba, tace"wlh kasan ba don hk ba kam sae don ra'ayi" Au haba naji nn yakai hannu da wasa zai ta6o qirjinta tayi saurin buge hannun tace"wea meye hk dan Allah" Bae kulata ba sae hannunsa yakai yana yawo dashi a hnkli kan jikinta yana yi kmr zai ta6o qirjinta sae kuma ya wuce zuwa bayan banta yana shafawa yayinda Rynt ke kuka tana buge masa hannu shi kuma yaqi ya daina har abun ya zamo musu kmr wasa,gashi still taqi yarda ta d'ago daga kan qirjinsa gudun kar ya ganta. Daina wasa yayi da jikinta ya d'ago fuskar ta yaga duk hawaye ce,yace"kinga zanyi magana dake amma bana son tsiwa mgnr hnkli nake so" Da kin min hk bazan takura ki akan dole sae kinsa bra ba"tace to ina jikinka" Sae da yakai hannu ya share mata hawaye snn yace"meyasa ba kya son saka bra ko kinada wata matsala ne? Tace"Aa ni kunyar ganin ta nakeji shiyasa bazan iya sawa ba" Yace"bazan 6oye maki ba kinada qirji mai kyau da bai kamata ace kin bar ya lalace ba don hk ki ajiye kunya ki fara bashi kulawar da ta dace" Shiru tayi don ita gabad'aya jin kunyar zancen sa ma take ji. Bai damu da jin amsar ta ba sae jayeta yake qoqarin yi daga jikin shi taqi yarda da hkn don sae qara 6oye qirjinta take a jikin shi,nn ya cire farar suit d'in jikin shi ya saka mata yana mae kallon fuskarta kmr wanda ke neman wani abu a jikin fuskar. yace"ba zancen school yau kin riga da kinyi letti don kar kice zaki tafi" Daga hk ya wuce ya barta nn tsaye wacce har ya fita kallon sa take snn ta kalli rgr jikinta da ya saka mata mae da'auke da wani irin qamshin dad'i. Fitowa tayi ta bar towel d'inta can ayashe , taje jikin wardrobe ta bud'e snn takai hannu jikin wata rgr atamfa har zata ciro sae kuma bata ciro ba ta rufe wardrobe kawai taje ta kwanta kan bed ta rufe jikinta da blanket har izuwa wuyanta daga nn ba jimawa bacci ya kwashe ta. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [10:11PM, 2/5/2017] Billy giro😊: [ 2/5/2017] ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮``` 🔮🔮🔮🔮 *page* *```45```* Man kuwa yana fita d'akinsa ya tafi ya sami malika zaune kan sofa tana shan 'ya'yan fruits yaje kusa da ita ya zauna ta kaimai slice d'in kankana a baki tare da fad'in"ya baka fita ba ko kun fasa ne? Eh an d'aga meeting d'in sae zuwa 12,tace"OK" daga hk suka ci gaba da shan fruits suna er firar su a cikin firar ne man ya d'auko laptop d'inshi yana nuna mata wasu kayan jarirai da ya gani masu kyau yace"duk a England ake samun su,tace "wow yaushe zamu je siyo kyn? Yace"na fison sae cikinki ya farà qwari muje har sae idan kin haifu snn ko zamu dawo amma zan riqa yi ina dawowa sbd aiki na,kiss ta d'aura mai tace"wnn ba matsala bane" Yayi d'an guntun murmushi yana ci gaba da nuna mata wasu kyn jarirai. Rynt kuwa ta jima kwance abinta tana baccinda ya mata dad'i fiye da kowanne. 11:30 Man ya shigo d'akin still sae bacci take,dube dube ya shiga yi ta inda zai ga suit jacket d'insa wanda har bathroom ya duba amma bae ganta ba. Hkn yasa yazo ya durqusa gab da ita yakai hannu ya d'an yaye mata blanket kad'an, nn yaga jacket d'in na jikinta hannuwanta na jikin qirjinta da ta kama magamar jacket d'in ta riqe gam. Ganin hkne yasa ya janye hannuwanta a hnkli ya rufe mata buttons wanda garin hkne ya hango d'an bum short d'inda ke jikinta kauda idonsa kawae yayi ya rufa mata blanket ya fita . Ba ita ta tashi ba sae qarfe d'aya. Ta tashi zaune tana mai kama mgmr jacket d'in,ga mamakinta taga an sanya mata buttons d'in rgr,ai kuwa taji fad'uwar gaba don tasan mohd ne ya shigo qila ma ya ganan mata jiki nn taji wani irin haushinsa ya kamata meye ruwansa da ita da har zai zo ya samu tana bacci ya yaye mata blanket har yakai ga sa mata buttons, ta buga tsaki tare da mamakin wane irin ma bacci ne tayi da har hkn ta faru bata jiba ita da sam bata da nauyin bacci . Rae 6ace ta d'auko towel ta cire jacket d'in ta jefar kan sofa snn ta nufi bathroom ta watsa ruwa sbd ta samu jikinta ya sake mata kan baccin da tayi. Koda ta gama shiri duk yunwa ta cika ta sae a lokacin ta tuna ko break fast ma batayi ba a nn ta kula da plate d'inta na break fast ,ta d'auki plate d'in ta fita ta kar6o wani abinci gun kuku. Sama sama ta samu taci abincin sbd tana jin jikin nata ba dad'i shiyasa ko cinye abincin ma ta kasa yi taje takai ragowar ta dawo har zata kwanta taji kiraye kirayen sllr zhr sae a lokacin ta kalli agogo taga biyu saura dama tayi arwala da taje wanka kuskure bakinta kawae taje tayi tazo tayi sallah. Tana idar da addu'a ta jawo pillow ta kwanta nn kan sallaya wacce sae son take ta tashi ta d'an dudduba littafanta amma tana jin kmr jikin bazai barta ba. Haka ta yini bata jin dad'i sae da tasha magani ne ta samu jin sauqi. Wacce har washe gari bata sake jin komai ba. Sae dai koda suka dawo school gabad'aya zazza6in ya dawo mata don ko uniform bata iya cirewa ba ta kwanta sae bacci. Mami kuwa ta cire uniform taje ta watsa ruwa ta saka er doguwar rgrta ta kanti da iyakarta guiwa taje d'akin yayanta ya bata abinci taci byn ta gama ya sama ta kallo nn malika taxo ta same su tace"my man wnn abar fa banga ta fito ba bare zancen d'aura min girki kuma kaga dae ba yanzun ne dawowar su ba zamanta ne kawae tayi "Yace"jeki zanje na taso ta " Nifa i cnt wait any more don yunwa nakeji sosai kuma kar ma mai lesson d'insu yazo ta wani ce zata zauna ma lesson ,hannun ta yaja suka fito yana mai fad'in "ai mae lesson d'in nasu bazai sami zuwa ba yau yayi tafiya" Ta6e baki tayi tace"hm lesson d'in ma nsn ba komai take ganewa ba don da gani kwañyar kifi ce da ita....wyr tace tayi qara tana ganin qawar ta faiza ce mae kiran ta nufi d'akinta shi kuma man ya wuce zuwa d'akin Rynt. Tsaki yayi ganin ko uniform bata cire ba amma tayi kwance tana bacci yace"lallai yrynr nn kinji dad'inki" Nn yaje yana tashinta da doka mata jiki ta tashi cikin mugun 6acin rae tana kallon shi tace"wae meye!? Yace"tambayata ma kike oya tashi kije ki d'aurawa malika girki" Tace"cab ni wlh bazan iya ba don bana jin dad'i" Yace"bana son raini maza tashi kije ki d'aura mata girki ko kuma wlh nayi maganin ki" Cikin marairaicewa tace"wlh bana jin dad'i ko tsayuwa ma fa da qyar nake yi" Yace"Bari kiji ko a kwance ne sae kin d'aura mata girkin stupid girl! Cikin muryar kuka tace"wae kai meyasa baka da tausayi ne,na gaya maka bazan iya ba bana jin dad'i wlh. Zowa yayi gab da ita yakai hannu ya d'ago fuskarta da kyau yana kallon ta yace"shin kin manta abinda na gaya miki ne na dole kibi abinda nace idan ba haka ba karatunki" Da mugun tsana take kallon shi tace a ranta _"mugu kayi abinka lokacinka ne nawa na nn zowa da zan rabaka da farin cikin ka gabad'aya don wlh bazan barka ba"_ Daga hk tafita ta bar shi tana saukowa downstairs ta had'u da malika wacce ta sha gabanta tana gaya mata maganganun banza. Tsaki kawai Rynt tayi ta ra6a ta gefenta ta wuce. Cike da azama malika tayi niyyar fizgo Rynt sae kawae ta hango man tafe nn tayi saurin sakin glass cup d'inda ke hannunta ya fad'i qasa ya tarwatse ta duqa kmr zata tsince glasses d'in dae dae man ya iso ya tada ta tsaye yana fad'in"ya akayi cup d'in ya fashe kuma har kk qoqarin saka hannun ki,da mamaki tace"hm wnn abar ce fa hk kawae ta biyo tamin muguwar bangaza ta wuce har ma tana fad'in wae zan gani" Yace"what! Tace"hm wlh" A fusace ya kama hanya zai tafi kitchen tayi saurin shan gabanshi tace"no my man kayi hqr ka barta kawae ni yanxu bana son wani tashin hnkli" Yace"da zanso naji me take nufi da zaki gani" common my man wnn abar me ta isa tamin ne shirme ne kawae take fad'i kaima ka sani,yi hqr kaji barta. Tsaki yayi yace "ya zama dole nayi maganin yrnyr nn sbd rainin nata ya fara isata" Tace"da Allah shareta ta zo muje" Nan taja shi suka je suka zauna kan two seater malika ta kira cleaners aka kwashe glasses d'in,snn ta kalli man tare da jawo hannunsa ta d'aura kan cikinta tace"my man wae nikam yaushe babyn mu zai fara motsi duk na qagu wlh" Wani murmushi yayi mae nuna jin dad'i har ransa yace"3 to 4 month ne yake farawa" Ta kalle shi zata ce wani abu knn wyrta tayi qara tana ganin qawar ta faiza ce tace da mohd "ina zuwa umma ce mae kiran" Bata jira me zai ce ba ta tafi. Tana shiga d'aki ta d'aga wyr . faiza"tace ya ake ciki ne kinsha maganin? Tace "Aa ynz nake shirin sha dae sbd so nake dai dai wnn abar ta gama min abinci maganin ya fara min aiki sbd zan fi son ina saka loma d'aya ta biyu sae kawae na fasa ihu kan aje asibiti na tabbatar cikin ya gama lallacewa,amma kuma wlh ina tsoron azabar da zanji kafin cikin ya zube Faiza"ta kwashe da dariya tace"kin fiye tsoro azabar da kwata kwata ta minti nawa ce yayinda ita waccan matsiciyar kin rabata da mijinki har abada" Tace"wlh kam yau dolenta ta rabu dashi,bari kedai nayi sauri nasha maganin kar taje ta gama abincin bansha ba,tace"ok bye sae mun had'u asibiti knn. Nan suka katse wyr malika ta ciro tablet a jakarta tasha snn ta fito ta sami man zaune inda ta barshi sae waya yake. Taje ta zauna kusa dashi tare da jinginwa a jikinsa wanda bae wani jima sosai ba ya gama wayar. Rynt kuwa da qyar taga ta kammala dafa indomie sbd wani irin bacci da takeji. Tana gamawa ta zuba indomie a plate ta fito wacce tun lokacinda ta fito kitchen man ke mata mugun kallo har ta qaraso gurin su,shi ya kar6i plate d'in indomie da taikaci yayinda Rynt bata damu da ganin yanda ya kar6i plate d'in ba tayi ficewarta ita dae ta samu ta ganta kan bed. Rynt na wucewa malika takai hannu zata kar6i plate d'in don har ta fara jin maganin ya fara mata aiki. Man yace"da zafi malika bari ta d'an sha iska tukun" Tace"my man yunwa fa nakeji sosai" Yace"Baza kici da zafi haka ba kam" nn gabanta ya shiga fad'uwa don in har yace sae abincin ya rage zafi asirinta zai iya tonuwa don gadan gadan ta fara jin maganin na mata aiki. Nan ta shagwa6e mae tace"pls my man kawae barni naci don zan ma fi jin dad'inta" Ba musu kuwa ya bata plate d'in ta kar6a ta fara ci tayi loma d'aya biyu a ta ukun ta ajiye plate ta fara riqe ciki man yayi saurin kallonta ya kuma kalli plate d'in indomie yace"lafiya? Tace"nima dae haka kawae ina fara cin indomie na fara jin cikina yana 6ird'a min" Yace"what!me tasa miki a indomien ne to? Bata iya bashi amsa ba sae zamewa tayi daga kan seater tana yarfi da hannu yayinda ta matse cikinta sosai da d'ayan hannunta. A take man ya rud'e ya jawota jikinsa ita kuwa sae ihu ta fara tana fad'in"wayyo my man cikina zan mutu na shiga uku ka taimaka min da magani nasha" Da sauri man ya tashi yaje d'akinshi yana shiga ya sami mami kwance kan sofa tayi bacci tana qoqarin fad'owa da saurin sa ya d'auketa ya maida kan bed snn ya d'auko magani da ruwa ya fito yana isowa ya saki magani har cup d'in ruwa sbd ganin yanda malika ta fara bleeding ba wata wata ya d'auke ta ya fita da ita yana qwalawa driver kira,driver yazo suka shiga mota aguje sae asibiti. Duk wani qoqari na ganin jinin ya daina zuba man yayi amma bai yi nasarar ceto cikin ba ya riga da ya zube,baqin ciki bai bar ya qarasa kula da malika ba sae wata docta yasa ,ya baro asibitin yayo gida a fusace wanda bai zarce koina ba sae d'akin Rynt riqe da belt a hannun shi. Rynt dake bacci sae saukar duka ta fara ji ta koina. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [10:27AM, 2/7/2017] Billy giro😊: [ 2/7/2017] ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮``` 🔮🔮🔮🔮 *page* *```46```* Cikin firgici ta tashi tana ihu tana neman guduwa man kuwa sae binta yake yana ci gaba da kai mata duka ta koina baji ba gani. Can ta samu ta fito d'akin aguje shima ya biyo ta yana duka harsuka sauko downstairs nn sukayi kici6is da umman saliha ta shigo ita da nasir,cikin kuka Rynt ta fizge daga hannun man zata je gun umman saliha kafin ta qarasa jiri ya d'ebe ta tafi suu zata fad'i umman saliha tayi hanzarin tarbota ta fad'a jikinta,yayinda nasir ke kallon man da mugun mamaki. Man kuwa qala bae ce dasu ba sae ma murtuqe fuskar sa da yayi ya fita yaja motar sa ya bar gidan. Umman saliha da ita ma duk mamaki ya cikata ta kalli nasir da yabi man da kallo tace"kama min ita mukai kan seater" Nan nasir ya kamata suka kaita kan 3 seater snn ya d'auko ruwa a fridge ya yayyafa mata,bata iya bud'e idonta ba sae ajiyar zuciya kawai ta ftr. Umman saliha ta kira sunanta kusan sau biyu amma Rynt bata amsa ba, nn umma ta kalli Nasir tace"ai da mun kaita d'akinta sae a kira Dr" Nasir yace"Aa umma kawae muje asibiti tukun daga can sae mu kaita gidan inna sbd nsn fa'iz mai iya zuwa ne yana ci gaba da dubata" Fa'iz ( cewa da wani abokin sa likita). Umman nasir tace"meyasa zamu kaita gidan inn ai sae hnklinta ya tashi kawai mu maida ta nn gdn in yaso kullum na riqa zowa ina dubata. Nasir yayi saurin yace"Aa umma baza mu maida ta gidan nn ba dmn wnn rashin tausayi da cin zali yayi yawa gsky bazan iya barin Rynt a cikin halin nan ba ai ko me ta masa bai kamata ace ya dake ta ba kodan kasancewar ta qaramar yarinya snn umma idan har kinzo da rana wa zai riqa kula da ita da dare har zuwa wayewar gari don wnn uban dukan rashin imani da ya mata ya kamata ace koyaushe tana da mae kula da ita shiyasa naga gsky ba inda ya dace aje da ita face gidan inna don shi dae na tabbatar bazai kula da ita ba. Umman saliha ta sauke ajiyar zuciya tace"shikenan nasir kamata muje mu saka ta a mota" Bayan sun saka ta a mota ne suka bar gidan suka nufi asibiti. Tafe suke kan hnya umman Saliha dake seat d'in baya rungume da Rynt sae kallon Rynt take cike da tausayi wacce in banda numfashi ba abinda take iya yi. Umman saliha ta nisa snn tace da nasir"ni ina mamakin wane irin abune Rynt tayiwa mohd da har ya iya mata wnn dukan" Nasir yace"ni nasan ba abinda Rynt ta masa da yakai ga duka kawae dae rashin imanin sa ne ya motsa,kuma umma dama fa Rynt zaman haquri kawae takeyi a gidan shiyasa nake son inna tasani ko hkn zai sa man ya daina quntata mata sbd idan inna taji tamkar Abbansa yaji ne , Abba kuwa kai tsaye zai gyara masa zamansa ne don bazai ta6a barin sa ya ci gaba da cutar da Rynt ba. Umma tace"lallai kam ba makawa zai gyara masa xamansa" Daga haka basu sake cewa komai ba sae Nasir da ya ciro wyrsa a aljihu ya kira abokinsa yana gama waya dashi se juya alkalar motar sa yayi zuwa canza hanya ummar shi ta tambaye shi lafiya yace"Fa'iz ne yace mu had'u can gidan inna sbd ya rigada ya baro asibiti. Tace" haka yafi sauqi amma hlnda inna zata ga Rynt nake tunani" Nasir bae ce komai ba don shima nazarin da yake yi kenan don yaso ace koda zata ga Rynt an ciyo kan matsalar sae dae kawae taji lbrn abinda ya faru. Suna isa shima abokin nashi na isowa. Dukkan su suka shiga gidan har shi fa'iz d'in wanda ga dukkan alama ya saba shiga gidan dan shine gaba sai sauri yake ya bud'ewa nasir qyallen qofa. Nasir dake d'auke da Rynt ya ajiye ta kan 3 seater abokin nasa ya shiga dubata sbd sunyi sallama har sun gaji ba amsa. Bayan abokin yayi en gwaje gwajen sa akan Rynt ya nemi akaita kan bed sbd yana son zai mata qarin ruwa . D'akin inna aka kaita snn aka d'aura mata ruwan sae a snn ne inna ta shigo gidan wacce ga dukkan alama maqota ta fito dan riqe take da qullin nono da fura a hannu,ai kuwa tana shiga d'akinta ta saki furar da nono tana taslima inda a rud'e ta shiga tambayar abinda ke faruwa da Rynt. Sae da nasir ya kwantar mata da hnkli snn ya snr da ita abinda ya faru. Kukan su na tsafi ta shiga yi tana sirfawa mohd zagi ciki da waje snn ta d'auko waya a cewar zata kira Abban mohd yazo yaga d'ayen aikin da yayi wa Rynt.....bata kae ga kiran sa ba taji abokin nasir na cewa da nasir "Haqiqa anyi babbar nasara dan duk irin dukan nn da tasha juna biyun da ke jikinta yana nn lfyrsa qalau" Da kmr mamaki Nasir yace"juna biyu ne da ita? Yace"tabbas kuwa tana d'auke da juna biyu don hk sae a kiyaye a riqa bata kulawar da ta dace" "InshaAllah" Shine abinda nasir yace kafin abokin sa ke rubuta masa magunguna ya bashi. Nn Nasir ya maida dubansa gun ummar sa da inna wad'anda kallo d'aya zakayi musu kasan sunyi farin ciki matuqa da jin zancen Dr musamman inna da kukanta ya koma dariya. Yace musu"zanje siyo magani na dawo" Inna tace"to d'an albarka sae ka dawo ,kai kuma Hafizu Allah sa ka gama da iyayenka lafiya don wnn lbr da na ji a bakinka ya kore min duk wani baqin ciki. Da shi har nasir sae da sukayi murmushi suka fita sbd fa'iz yasha fhmtar da ita sunan shi amma sae tayi ta kiran shi da hafizu tun yana gyara mata har ya daina sae dae kawai yayi murmushi idan ta kirashi da Hafizu. Suna fita inna taje kusa da Rynt dake ta sharar bacci tace "um! um! baiwar Allah, Allah iskar miki ga shashan yaron nn muhammadu ai zai zo ya sameni ne zai kuma had'u da ubansa kabiru dan sae na snr dashi komai kaf ba abinda zan rage shashan yaro kawai marar tausayi da baisan daraja mace ba. Nn ta d'auki fura da nonon da tayar a kan fridge wad'anda umman saliha ce ta d'auke ta d'aura akai. Ta d'auki furar tana mae fad'in"bari naje na dama ma er albarkar nn Rynh ita kafin ta tashi tayi sanyi sae tasha" Tana gama fad'ar hk ta kama hnyr fita d'akin umman saliha ta tashi da sauri tana qoqarin cewa da inna ta kawo furar ta dama sae ga man ya shigo d'akin shaye da toka riqe da mami a hannun shi wacce taje da gudu kan jikin mamarta. Mohd kuwa yana had'a idô da inna ya wani qara d'aure fuska dan karma inna taga damar shi . Amma hkn bai hana inna ta shiga sirfa mae masifa tana"fad'in shashan yaro me kuma ya kawoka ko kazo ka qarasata ne iye! Komai mohd bai ce da ita ba sae zuwa yayi kan gadon da Rynt ke kwance ya ajiye wata farar takarda ya fita . Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [11:03PM, 2/8/2017] Billy giro😊: [2/8/2017] Billy giro😊: ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮``` 🔮🔮🔮🔮 *page* *```47```* Inna tace yau naga shahan yaro me kuma ka ajiye mata kan gadon da har ina ma magana zaka wani wuce ni. Nn umman saliha ta tashi taje ta d'auki takardar ta karanta wacce tana gama krntawà ta saki takardar ta zauna sakwaf kan gado tana taslima had'e da fad'in innalillahi wa inna ilaihi raji'un! A rud'e inna ta d'auki takardar tace"lafiya me ya rubuta mata a takardar ne? Umman saliha tace"saki ne inna! Da qarfi inna ta dafe qirjinta tare da fiddo ido waje tace"saki! Sae kawai ta fashe da kuka tana"fad'in innalillahi wa inna ilahi raji'una anya kuwa muhammadu yana son ya gama lfy, me wnn er albarkar ta masa da zai had'a mata zafi biyu a lokaci d'aya nn ta koma fashewa da wani kuka inda cikin kukan ne ta kira Abban mohd ta snr dashi komai. Kafin yazo sae ga nasir ya dawo da siyen magani ya qaraso jiki sanyaye ganin yanda inna keta fmn shar6ar kuka har da su fyace majina, a hnkli ya ajiye ledar maganin hannunsa kan bed yaje ga inna yana tmbyr me kuma ya faru? Takardar hannunta ta miqa mae tace"gane ma idonka abinda d'an banzan yaron nn ya rubutawa Rynh ,yana kar6ar takardar ya hango saki 6aro 6aro nn ya cire hular kanshi tare da kallon Rynt dake kwance still tana bacci yace"ya saketa! Daga nn shima ya zauna gefen gadon dafe da kai yana tunanin me Rynh ta ma mohd ne wae. Yana cikin hkne yaji sallamar Abban mohd. A hnkli ya d'go tare da zamewa kan gadon ya durqusa yana gaida shi ya amsa ba yabo ba fallasa yayinda ita ma umman saliha ta gaida shi ya amsa snn suka fito d'akin suka barshi shida inna. Cikin damuwa Abban mohd yaje gun Rynt yana mae kallon yanayinda take ciki can ya nisa yace da inna"shi mohd d'in bai ce ga abinda ya had'a su bane? Inna tace"meko yace sae shigowa kawai da yayi yaje ya ajiye mata takarda ya fita wanda har ma magana nake masa amma yaqi ko kulani. Abba ya jinjina kansa snn yakai hannu ya ciro wyrsa a aljihu ya kira mohd Yana d'agawa yace"duk abinda kake ka ajiye shi kazo ka sameni a gidan inna. Daga hk Abba ya katse wyr. Mohd dake zaune a asibiti gurin malika wacce tasa shi gaba tana ta kuka wae ita kukan baqin cikin zubewar cikinta take yayinda shi kuma duk ya wani sukui kuice yana fmn lallashinta. Shine ya samu da qyar ya lalla6ata tabar shi ya fita. Fa'iza wacce daman tana cikin d'akin. Tana ganin mohd ya fita taje ta ba malika hannu suka lale ,malika tace"Abbansa ne ya kira shi nsn kan sakin nn ne da yayiwa wnn abar " Faiza tace"hln bai ji dalilin sakin bane? Ta6e baki malika tayi snn tace"oho masa nidai tunda buqata ta riga ta biya komai yayi" Faiza tace"wae dae tukuna saki nawa ne ya rubuta mata" Malika tace"har kya tambaya ai kinsan uku ne ba tantama,shiyasa kika ji nace buqata ta ta gama biya don ba zancen ace ya maida ta kuma sun rabu knn har abada yayinda ni kuma zan zame masa mutu ka raba takalmin kaza. Nan suka koma lalewa suna kyakkewa. 6angaren mohd kuwa da isar shi gidan inna kai tsaye ya tafi sae d'akinta ya samu guri a qasa ya zauna yayinda inna ke zaune kan bed Abbansa kuwa yana kan sofa. Abba ya kalle sa da kyau snn yace"Ashe baka da hnkli ban sani ba mene ne ya had'aka da Rynt da har ka iya dukanta ka kuma had'a ta da takardar saki? Shiru mohd yayi . A fusace Abba yace"shin bada kai nake magana bane! Kallon mahaifin nasa yayi ya koma duqar da kanshi qasa snn yace"Abba da ka bari idan ta farka sae kaji a bakinta" Abba yace"don uwarka ni sa'an ka ne da zan tambaye ka kace min na bari har Rynt ta farka ,kai dai zaka gaya min d'an iskan yaro kawai shashasha wanda baisan darajar mace ba,wae karasa inda zakayi zalunci sae akan mace. Ran mohd ne ya soma 6aci da jin irin zagin da Abba ke mae ya daure yace"Abba ka daina ganin laifina akan abinda baka ji ba, yrnyr nn fa kwata kwata bata da gsky haka kuma hkncin da na d'auka akanta shine dai dai " Abba yace" wane laifi ne Rynt zata maka da zata ci wnn banzan hukuncin naka na masara imani da rashin tausayi" Mohd Yace"Abba cikina ta 6arar min dake jikin malika ta hnyar sanya mata magani a abinci" Cikin d'aga murya Abba yace" sam! wnn qarya ne kwata kwata Rynt bazata aikata hk ba idan har zarginta kake to kayi gaggawa cirewa" Abba ba zarginta nakeyi ba ta aikata ne don a gaban idona komai ya faru.....Qarya kake munafukin Allah Rynt bazata ta6a aikata hk ba kawae dama can ba son auren nata kake ba shine ka 6ullo da wnn hnyr na ganin ka yakice aurenta dake smn kanka to kasani wlh daga yau kar na koma ganin qafar ka a gidana tunda ni ban isa da kaiba koma nace baka d'auke ni a uba ba,don hk sae ka nemi wani uban bani ba! Cikin fad'a ita kuma inna ta kama da cewa"marar kunyan yaro da baka santa meyasa to ka mata ciki! Da sauri mohd ya d'ago ya kalli inna yace"ciki" Inna tace"eh ko kuma cewa zakayi bakai kayi cikin bane iye! Sadda kansa kawae yayi qasa ba tare da yace komai ba. Abban sa ya daka mae tsawa yace"ka bata amsa mana bada kai take magana bane! Yace"nawane" Shi ne kad'ai abinda yace Yayinda Abba yace"oya maza tashi ka bamu guri shasha! kuma wlh kasani har nn gidan d'in ma ban yarda ka sake tako qafar ka ba kaji na gaya ma! Daga hk Abba ya fita fuu yana mae gyara babbar rgr shi wanda yana kai falo yace da nasir"ina son gobe da safe kaje gidan nashi ka kwaso kaf kyn Rynt kazo dasu nn gidan" Da ladabi nasir yace"to" Snn Abba ya fita haka shima man ya fita yabar gidan cike da tunanin cikin da ke jikin Rynt. 9:00pm Rynt ce ta shiga motsi a hnkli inna dake gefenta tayi hanzarin matsawa kusa da ita tace"Rynh kin tashi? Komai Rynt bata ce ba sae yunqurin tashi zaune take nn inna ta taimaka mata ta tashi zaune. Snn inna taje da hnzri ta bud'e fridge ta d'auko damammar fura a cikin kwanan shan ruwa wacce umman saliha ce ta dama ta kafin ta tafi. Ta di'bar wa Rynt a kofi taje ta kai mata ,Rynt takai hannu ta kar6i kofin furar tana mae kallon inna' Inna tace"Sha kinji Rynh" ba musu takai kofin fura a bakinta tasha kad'an tace"inna bana son furar idan da kunu zan sha amma nafi son mai d'an tsami da sanyi" Inna tace"Rynh za'a sami kunu mai sanyi amma baya da tsami sbd d'azu da rana Baaba hurare ta daman min shi sae dai idan kina so na sa maki ruwan tsamiyà a ciki" Tace"Eh inna ina so" Nn inna ta kar6i kofin furar ta saka shi a fridge snn ta fita zuwa kitchen ba jimawa sae gata ta dawo d'auke da kofin kunu ta ba Rynt wacce ta kar6a ta shiga sha" Inna kuwa ta d'auko magunguna tana 6alla mata kmr yanda nasir ya gaya mata kafin ya tafi. Tana gama 6allewa ta ba Rynt ta kar6a tasha snn ta tashi ta nufi bathroom tayo arwala tazo tayi sllr dake kanta . Washe gari Nasir ne ya shigo gidan shida abokin sa fa'iz . Da shigar su suka had'u da inna ta fito kitchen d'auke da ruwan zafi a cup zata had'awa Rynt shayi,sun gaidata had'e da tmbyrta mai jiki. Tace "Alhmdlh mu shiga tana daga ciki" Nn suka shiga suka sami Rynt kan gado ta had'e kai da guiwa. Sallamar su yasa ta d'ago ta d'an saki fuska ta musu ina kwana suka amsa tare da fad'in ya jikin naki? Tace"Alhmdlh" Faiz yace"da akwai abinda ke maki ciwo ko kuwa" Tace"Aa ba inda ke min ciwo kawai...sae tayi shiru. Yace"zafin duka ko? Kai ta gyad'a mishi tare da qoqarin mayarda hawayen da ke son zubo mata" Fa'iz yace"kici gaba da shan magunguna kafin gobe inshaAllah zaki ji jikin ki dai dai kinji" Tace"to" Snn nasir yace"jiya kinsha magunguna? Tace"eh inna taban" Yace"to yau fa" Tace"tukuna ban sha ba" Inna dake zuba madara a ruwan tea tace"ai yanzu nake shirin d'auko mata magungunan idan ta gama shan shayi sae tasha" Nasir yace"To inna mu zamu d'an fita mu dawo" Tace"to d'an Albarka sae kun dawo" Nan suka fita inna ta bawa Rynt shayin da ta gama had'a mata snn ta d'auko mata magunguna had'e da kofin kunu ta ajiye mata,taje ta bud'e fridge ta d'ibi fura ta zauna zata sha knn sae taji sallamar Abban nasir. Washe da baki ta fita ta same shi a falo yayinda shi kuma yana ganin ta ya durqusa har qasa yana gaida mahaifiyar tashi. Bayan sun gama gaisawa ya koma kan cushion ya zauna itama inna ta nemi guri ta zauna. Yace"inna ya jikin Rynt? Tace"taji sauqi don yanzu haka ma karyawa take,ko na kira ma ita ku gaisa ne? Eh inna don akwai mgnr da ma nake son nayi da ita. Nn inna ta qwalawa Rynt kira wacce sae da ta amsa kiran snn taxo falon ta durqusa cike da ladabi ta gaida Abban nasir. Byn ya amsa yake cewa"Rynh ina so zan tambaye ki ne,shin meye ainihin abinda ya had'a ki da mohd? A sanyaye tace"Abba ni ban san na masa komai ba kawai ina cikin bacci naji yana dukana amma banda shi ba abinda na sani" Abban nasir ya nisa yace"amma kuma mohd yace abu kika sawa mtrsa a abinci taci cikinta ya zube" Da sauri Rynt ta kalli Abban nasir cikin muryar kuka tace"wlh Abba ba haka bane ni ba abinda nasa mata a abinci" Shiru Abban nasir yayi can yace"shikenan tashi tafiyarki" Rynt ta tashi tana mae share qwalla ta koma daga ciki. Bayan ta shiga ciki ne taji Abban nasir na cewa da inna"ni na rasa gane kan wnn al'amarin shi mohd da na kirashi na tambayesa har rantsuwa yamin kan cewa a gabon idonsa malika taci abincin da Rynt ta dafa ta kawo mata wacce ko spoon uku bata samu tayi ba cikin ta ya shiga 6ird'a daga hk ne ta soma zuvar da jini ya kwashe ta zuwa asibiti wanda koda suka isa cikin ya riga da ya zube bai iya ceto rayuwar abinda ke cikin ba" Inna tace"yo kae ka yarda da zancen nasa knn ni nsn ba wani ciki da mtrsa keda makirci ne kawae suka qulla shida mtr tashi na ganin sun fitar da Rynh a gidan. Abban nasir yace"kodai mtr tasa ce ta qulla makircin don bana tunanin mohd zai biye wa shirmen mata har a had'a irin wnn makirci dashi......yo tunda ba son auren yake ba ai zai biye mata ne. Yace"to inna abar wnn zancen ni yanzu abinda nake so shine a sasanta tsakanin su, Rynt ta koma d'akin mijinta tunda saki d'aya ne ya mata.....yo so kake ta koma ya idata knn in yaso na rasa abinda zan cewa mai garinsu da ya damqa min amanar ta, to ba'ayi hk dani ba, fatana Allah ya sauke ta lafiya ya bata wani mijin mae sonta tsakani da Allah wanda kuma zai riqe ta da gsky,ba irin shashashan yaron nn da ba abinda ya iya sae cutar da ita ba. Abban nasir yace"inna ki daina wnn zancen dmn ba abinda yafi dacewa irin a maida Rynt d'akin mijinta ko don qaruwar da suka samu a tsakanin su. inna tace"kaga Bello idan wnn zancen kad'ai ya kawo ka gidan nn gwara ka tashi ka tafi don Rynh kam bazata koma gidan wnn marar imanin yaron ba,idan kuwa ka koma zowa ka matsa min da zancen wlh zan d'auki Rynh ne mu koma can qauyen nasu da zama kuma ba wanda yà isa ya sani na dawo. Haquri kawae Abban nasir ya bata ya fita ya bar gidan cike da damuwa. Inna kuwa rae 6ace ta koma d'aki ta sami Rynt sae kuka take kmr ranta zai fita wacce ba komai take yiwa kukan ba sae jin cewa tana d'auke da ciki. Inna kuwa ba abinda ya fad'o ranta sae tunanin ko qazafin da mohd ya mata ne take yiwa kuka. Nan taje gun Rynt sae dae kafin tace komai Rynt ta kalleta cikin kuka sosai tace"dan Allah inna kisa a cire min cikin nn wlh nayi qanqanta,dmn nasan mutuwa kawae zanyi gurin haifuwa" Inna tayi er dariya tace "Rynt bazaki mutu ba zaki haifu lafiya kinji" Tace"amma inna karatu na fa? Tace"zaki ci gaba da karatun ki a nn kinji" Inna to ta yaya zanyi karatu da ciki wlh kinsan da kmr wuya dan Allah kisa a cire min inna " Inna tayi shiru tana kallon Rynh sae can tace"bazan 6oye miki ba Rynh kinzo dani gaa6ar da bazan iya ba don har gwara ma kice min kina son komawa gidan muhammadu da kice min a cire wnn cikin. Daga hk inna ta tashi tabar d'akin. Rynt kuwa ta qara fashewa da wani sabon kuka dan ganin take shike nn man ya 6ata mata tsarin rayuwar ta,ya kuma lalata mata duk wani lissafin karatun ta. Lallai idan ba'a cire mata cikin nn ba,ba abinda yafi cancanta a gareta yanzu shine ta d'auki fansar ta kawae ta qara gaba. Duk a cikin kukanta ne take wnn tunanin . Yayinda inna ta dawo d'akin tana ta bata baki amma Rynt bata iya daina kukan ba don ma yini zungur ta kwashe tana abu d'aya. Ai kuwa duk inna tabi ta damu sosai sbd ko abinci Rynt taqi ci wacce ko karin kumallon da ta fara da safe bata qarasa ba. Cikin hkne nasir ya fad'o gidan inna ta tarbe shi da cewa"yauwa Nasiru dama kai nake shirin kira yanzu. Yarinyar nn Rayyanah tun d'azu sae kuka take tayi ita sae an cire cikin da ke jikinta, ko abinci taqi taci tun safe har yanzu. Nan nasir ya tambayi inna ko meye dalili , Inna ta gaya mae duk yanda sukayi da Rynt. Yayi shiru snn yace "bari naje gurin ita Rynt d'in" Bai jira me inna zata ce ba ya shiga inner room ya sami Rynt zaune kan sallaya ta had'e kai da guiwa tana ta kuka. A hnkli nasir yaje ya durqusa kusa da ita tare da kiran sunanta Nn ta d'ago a hnkli tana kallon shi da jajayen idanuwanta da duk suka kumbura yace"kukan ya isa haka indae ciki ne zan sa a cire maki kinji" Cikin dasasshiyar muryar ta da tasha kuka tace"nagode" Yace"to share hawayenki" Ba musu takai hannu ta share hawayenta Yace"kici abinci kuma kisha magani idan na dawo gobe sae naje dake a cire cikin ko" Nan ta gyad'a mae kai shi kuma ya tashi ya fita, yaje ya sami inna yace "inna shikenan ta daina kukan yanzu kije ki bata abinci taci" Inna ta washe baki tace"yo kai Nasiru me kace da ita ne da har tayi shiru kai tsaye? Murmushi yayi yace"inna ina sauri yanzu amma gobe idan na dawo mayi magana" Tace"to d'an albarka Allah kaimu goben" Nn ya fita inna kuma ta shiga d'aki washe da baki". Billy Giro😊 [10:12PM, 2/9/2017] Billy giro😊: [ 2/9/2017] ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮``` 🔮🔮🔮🔮 *page* *```48```* Ta sami Rynt ta tashi tana linke carpet d'in sallah. Inna ta kar6i carpet d'in ta koma shimfid'a mata a nn kusa da gefen gado tace da ita "zauna bari naje na kawo maki abinci kici ko" Rynt ta gyad'a mata kai snn ta zauna, inna ta kai hannu nn kusa da bedside drawer ta d'auki abincin rnr da Rynt bata ci ba taje dashi kitchen ta kawo mata tuyon shinkafa da miyar ganye wacce taji qassan nmn rago . Ta kai kusa da Rynt ta ajiye snn ta kawo mata ruwa da kunu da magunguna a cewar idan ta gama cin abinci sae tasha. Sae da Rynt ta yiwa inna godiya snn ta kai hannu had'e da bisimillah ta fara cin abinci. Da ta kammala ne takai kwanika a kitchen ta dawo ta fad'a bathroom tayi wanka koda ta fito ta sami inna na waya cike da murna tana gama wyr ne take ce ma Rynt"Ashe saurin da na Nasiru keyi fatima ce a asibiti shine yanzu aka kirani aka snr dani ta sauka lfy ta sami d'a" Rynt ta d'an saki fuska snn tace"to Allah ya raya masa shi akan sunna" Inna ta washe haqora tace"Amin amin ai ba dan dare ba da naje naga sabon mae gidana" Murmushi kawae Rynt tayi taje ta nemo kyn bacci ta saka ta kwanta. Washe gari Rynt taji sauqi sosai don ita ma ta gyare gidan tsaf ta kuma je kitchen tana ragewa Baaba hurera aiki wacce tana zowa bata fara aiki ba suka tafi gidan su mohd gun barkar pretty ita da inna. Tana cikin aikin ne suka dawo Baaba hurera ta shigo tana mata sannu da aiki snn tace taje inna na kiranta a falo. Koda taje falon ta sami inna da Abban mohd taje ta durqusa cike da ladabi tana gaida shi ya amsa mata cikin sakin fuska snn yace"ya jikin naki? Tace"Alhmdlh"snn yace"dama zançen karatun ki ne tunda kinji sauqi gobe zan turo driver wanda zai riqa kai ki makaranta yana maida ki,snn kmr yanda ake maki lesson a can gidan nn ma zan nemo maki wanda zai riqa zowa yana maki lesson d'in,snn kuma duk wani abu da kk buqata ki snr da inna sae ta snr dani" Tace"to Abba nagode" Yace"shikenan tashi ki tafi" Bayan ta wuce ne ya ciro kud'i a aljihun sa bandir d'in 1k guda biyu yaba inna yace"d'aya naki ne d'aya kuma ki riqa bawa Rynt d'ari biyar biyar duk safiya ta na samun na cin abinci idan taje mkrnta dn naga mkrntar tasu yini ake" Ina ta kar6i kud'in had'e da sa mishi albarka yace"nagode inna ni zan tafi" Tace"to d'an albarka Allah kai ka lfy" Yace"amin" snn ya fita. Ita kuma taje d'aki ta adana kud'in. ***** Kwance yake kan bed sanye da farar singlet da farin boxer malika ta shigo d'akin ta kalli yanda ya d'ora qafa kan qafa yana mai kallon silin. Taje ta zauna kusa dashi tana mai kallon fuskar shi snn tace"my man ya kamata ka haqura ka daina tunani akan rashin da mukayi,ai Allah zai sake bamu wani ne komai baqin cikin wnn abar kuwa. Lumshe idonsa kawae yayi ba tare da yace komai ba tace"ya zancen zuwa gidan naku ? Yace"ki tafi kawai" Tace"baza kaje ganin jariri ba knn ? Kallonta kawae yayi bai ce mata komai ba sae kwanciyar sa da ya gyra. Tasan ba amsar zata samu ba shiyasa kawae ta tashi tabar d'akin taje ta shirya ta fita. Gidan su man d'in ta nufa wacce da shigar ta 6angaren su man kai tsaye ta haura sama zuwa d'akin mhfyr man ta bud'e qofar d'akin ta shiga ba ko sallama,pretty dake zaune kan bed tana shayarwa ta saki murmushi tace"sae yanzun" Sae da malika ta zauna snn tace"hm nida nake ganin ma nayi sammako" Pretty ta bata jariri tare da fad'in"yaya fa? Tace"wlh yana can cikin damuwar rashin babyn mu har magana ma bai cika son yi ba" Pretty ta cije le6e tace"wlh Allah matsiyar yarnr nn taci uban rainin wayo! ni kuna me wae ma har tayi nasarar 6arar miki da ciki? Malika ta ta6e baki had'e da murmushi snn ta duba koina idan ba mai ganin su ta kai bakinta a kunnen pretty ta rad'a mata magana ,pretty ta fiddo ido had'e da washe baki snn tace"kai haba! malika tace"Allah kuwa snn tace"amma fa bakin ki qanin idonki wlh kar ki bari kowa yaji zancen nn don ina gudun ya koma kunnen yayanki" Tace"haba dan Allah sae kace ban san me nakeyi ba ai ko umma bazata ji wnn zancen ba,,kuma kin san Allah da har kin ban haushi da naga na koma kai miki magani amma naji shiru ashe kinsan abinda kk shirin yiwa matsiyaciyar. Malika tace"ai ke ajiye maganin gefe nayi nace sae na gwada plan d'ina tukun. Pretty tace"shiyasa da muka je dubaki lkcn da umma keta masifa tana fad'in duk laifinki ne dan da kinsa mata maganin a abinci taci ta haukace da duk hkn bata faru ba sae naga kin kalle ta kawae kinyi shiru . Malika tayi dariya tace"wae ina umma take ne ma? Pretty tace"Wlh tana kitchen da fitar ta mane ba jimawa se kika shigo. 8:30pm Inna ce zaune a falo ita da Rynt suna cin abinci bayan sun gama Rynt tace"inna nifa gobe bana da kayan sawa idan zanje makaranta duk suna gidan can" Inna tace"ayyo ai tuni an kwaso maki kayanki suna a d'akin ki nasa nasiru yakai , ai a cikin kayan ne ma na d'ebo wasu en kyn sawa nakai miki a d'akina" Tace"inna kayan mami fa? Tace"yo ai kaji fa amma bari na kira nasiru naji da yaje kwaso maki kaya har da kayan mami ya kwaso ya had'o ko kuwa" Nan ta d'auki wayarta ta kira nasir bayan sun gama wyr ne tace ma Rynt yace duka har kyn mami d'in ya had'o ya kwaso wanda tun d'azun yaso yazo ya d'auki kayn nata yakai gida sae bae sami lokaci ba amma yace yanzu zai zo ya d'auki kayan" Rynt tace"to bari naje na had'a masa kayan kafin ya iso" Inna tace"to" Snn Rynt ta tashi ta nufi d'akinta da take zama a daa. Kan gado ta sami kayan nasu komai har akwatinan lefenta wad'anda kallo d'aya ta musu ta kauda idonta ta d'auki akwatin mami ta bud'e taga komai nata na ciki ta rufe akwatin ta ajiye ta gefe kusa da qofar d'akin snn taje ta bud'e akwatin ta wacce inna ta saya mata ta samu itama komai nata na ciki zata rufe kenan akwatin ta sa6ule ta fad'i sae duk kayan suka fita nn ta hango tsofuwar ajiyar ta ,ta kai hannu a hnkli ta d'auki viva ledar ta bud'e . Kayan da marigayi anwar ya bata ne a ciki nn ta shiga ciro kayan d'ai d'ai tana kallo. Hawayenda suka cika mata ido ne suka shiga gangarowa a hankali yayinda ta ciro bandir d'in 1k guda biyu masu d'auke da jini a jikin su nn taji inna ta qwala mata kira tayi saurin mayarda kud'in har kynda anwar ya bata snn ta amsa kiran da inna ke mata had'e da share hawaye ta kama hanya zata fita sae ga nasir ya shigo d'akin yace"har kin gama had'a kayan? tace"na samu kayan a had'e suke" Yace "eh hkne ni na had'a kyn tun can sbd a wardrobe d'inta na sami akwatin ta shine na saka mata duk kayan da ke cikin wardrobe d'in haka kema" Tace"mungode" Snn yace"zancen da mukayi jiya dake ban manta ba ina son sae na sami lokaci ne sae nazo muje a cire cikin ko? Tace"to" Yace"yauwa sae ki maida hnkli ki ci gaba da zuwa mkrnta kinji" Nn ta gyad'a mishi kae shi kuma yaja akwatin mami ya fita. Ita kuma taje ta gyra kayan akwatinta da suka zube ta rufe sae dae kafin ta rufe akwatin sae da ta cire kynta na zuwa school ta d'auke su ta tafi dasu d'akin inna. 12:00 na dare Man ne ya fito d'akin shi wanda bai zarce koina ba sae d'akin Rynt . A nn bakin qofa yayi tsaye yana qarewa d'akin kallo sae can ya qarasa shiga d'akin yaje gun wardrobes ya bud'e yaga ba komai kaf an kwashe ya maida wardrobes d'in ya rufe . Har zai fita sae ya hango farar suit jacket d'inshi kan sofa yaje ya d'auki jacket d'in a hnkli yana kallo, Se kuma yayi saurin kauda idonsa kan jacket d'in ya kuma jefar da ita kan sofa ya fita. Washe gari da safe Rynt ce ta kammala shirinta tsaf na school inna ta ciro d'ari biyar ta bata Rynt ta kar6i kud'in tace"ba canji ne inna? Inna tace"canjin me kud'in ki ne fa da zaki tafi dasu makaranta na cin abinci ko basa isar ki? Rynt ta bud'e ido tace"inna ai kud'in sunyi yawa ai d'ari biyu ma sun isa kuma ina ma da kud'i a hannu na da kin barshi kawae inna" Inna tace"yo Rynh kud'in hannunki ai naki ne,wad'an nn kuma na cin abincin mkrntr ki ne kabiru ya bayar a riqa baki" Tace"to inna nagode amma dae zan dawo da sauran canji dan sun min yawa" Inna tace"to er albarka a dawo lafiya Allah tsare min ke ya kuma bada sa'ar karatu" Tace"amin inna"snn ta fita ta samu driver na jiranta a qofar gida taje ta shiga motar yaja suka tafi. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [10:23PM, 2/10/2017] Billy giro😊: ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮``` 🔮🔮🔮🔮 *page* *```49```* Ana sauke Rynt a school sae kawai taji ihun mami tazo aguje ta rungumeta. cike da murmushi Rynt ke kallonta tace"mami kece waya ya kawo ki? Washe da baki tace"Abbana ne yanzu ya wuce" Sae kuma tasha toka tare da fad'in"Anti wae meyasa kika koma gidan inna da zama? Rynt tayi shiru tana kallonta can tace"to ai dama can gidan inna nake zama ko kin manta" Tace"Aa ni nafi son ki koma gidan yaya sbd na fi son a riqa kawo mu school tare" Rynt tace"ai ko ba'a kawo mu tare ba, ba gashi muna had'uwa ba" Turo baki tayi tace"um um anti hk ba dad'i" Rynt tace"kinga jeki 6angaren ku za'a fara assembly kar kiyi letti kinji" Mami tace"to Anti gsky ni sae kin gaya min yaushe zamu koma gidan yaya" Rynt tace"to kisa ido duk rnr da kika ga raqumi ya shiga akurki kizo da gudu ki gaya min sae mu koma ko" Da murna mami tace"dgske anti! Rynt tace"eh" Mami tace"meye ma raqumi wnn abun mae girma kmr doki ko" Rynt tace"eh" Mami ta daka tsalle tace"Allah kuwa da jimawa na ta6a ganin shi hnyar kasuwa,gobe ma zan cewa umma muje kasuwa da na ganshi zanyi ta kallon shi har sae naga ya shiga akurki sae nazo har gidan inna na gaya miki,sae mu koma abin mu gobe gidan yaya ko. Rynt tayi murmushi had'e da girgiza kanta ta tafi tana fad'in"to naji zan neme ki a break" Tace"ok anti bye" 5:00pm Rynt ce ta dawo daga mkrnta ta sami inna a falo duk ta raja'a gun kallo har sallama tayi kusan sau biyu amma bata ji ba, tayi tsaye d'auke da murmushi tana kallon inna snn taje a hnkli kan jikin inna ta rungumeta, a tsorace inna ta juyo ganin Rynt ce ta sauke numfashi tace"yo Rynh kece aini har kinsa na tashi guduwa , Rynt tace"haba dae inna da tsufanki kk shirin guduwa?inna tace"yo ai shi tsoro ba ruwan shi da tsufa " Dariya Rynt tayi tace"hln ma meya tsorota ki ne inna? Tace"yo Rynh ina zaune qalau kawae naji an hau kan jikina bayan nsn ni kad'ai ce a falon ban kuma ji shigowarki ba Tace"to inna ai nayi sallama har sau biyu kece dae bakiji ba sae kallo kike tayi abinki" Inna tace"ayyo inafa zanji na maida hnkli gun shiriritar banzar nn da ba zata fisshe ni ba" Murmushi kawae Rynt tayi ta tashi tare da fad'in "inna ni zanje na d'an watsa ruwa" Tace"to er Albarka sae kin fito" Nan Rynt ta wuce inna kuwa taci gaba da kallo. Tana gama wanka ta shirya ta ciro wata baqar leda a cikin jakarta ta mkrnta ta fito ta tafi kitchen sae gata ta dawo d'auke da agwalima cikin bowl. Taje ta zauna qasa kusa da kujerar da inna ke zaune akai ta d'auki d'aya zata fara sha tare da fad'in" inna ga agwalima" Inna tace"yo Rnynh ni na d'auka ko abinci ne kika d'ebo" Tace"Uhm agwalima ce na wanko na d'an sha ko d'aya ce sae naci abinci " Inna tace"lallai kam ki hanzarta kici abinci kafin mai miki dasarin yazo" Tace"inna ni idan ma da fura ita kawae zansha ba sae naci abinci ba dan bana jin yunwa" Tace"to tashi kije ki d'ebo furar tana can a cikin firijin tayi sanyi kuwa. Ba musu Rynt ta tashi ta d'ebo furar tazo tayi zaune ta shanye agwalimar hannunta snn tasha fura tana gamawa taje ta had'o komai nata na lesson ta fito ta samu inna na kar6a sallama inna na ganinta tace yauwa je d'auko tabarma don inaga mae miki dasarin ne yazo,nn Rynt ta koma d'aki ta d'auko tabarma ta fita. 6angaren mohd kuwa kwance yake a falo shi kad'ai kan 3 seater ya lumshe ido kmr mae bacci. Da damuwa ya bud'e idonsa had'e da guntun tsaki sbd door bell d'inda yaji ana fmn dannawa kan dole ya tashi yaje ya bud'e qofa, ganin wanda ke tsaye yasa ya d'an saki fuskar shi ya bashi hannu suka gaisa har yana masa ya hanya. Wanda ba kowa bane face lesson teacher d'in su Rynt wanda tun lokacinda yayi tafiya sae yau ne ya dawo. Man bai iya bashi hanya ba sae nazarin abinda zai ce masa yake can ya kallesa yace"kayi hqr fa yaran basa nn sunyi tafiya" Lesson teacher yace"to shikenn amma yaushe ne zasu dawo? Shiru man yayi can yace"ka tafi kawae dae" Ba musu lesson teacher d'in yayi sallama dashi ya wuce. Man ya rufe qofar ya juya ya sami malika a tsaye tace"my man waye ne? Yace" Lesson teacher ne Tace"au shi baisan matsiyaciyar tayiwa kanta tsiya ba" Komai bai ce da ita ba sae zama yayi ya jingina bayansa tare da lumshe idonsa . Nn taje ta zauna kusa dashi tare da kwanciya kan qirjinsa yace "pls malika im nt in mood n i just wnt me alone ki tafi d'akin ki kinji " Zata ce wani abu knn yace"pls just go" Jiki sanyaye ta tashi ta tafi zuwa d'akinta,haka shima ya tashi ya bar falon ya tafi d'akin shi. 2 dayz later haka mohd ya cigaba da rashin son damuwa komai qanqantar ta kuwa shiyasa ko yaushe yafi son ya kasance shi kad'ai wanda ko asibiti yaje baya wani jimawa yake dawowa. Rynt kuwa sae karatun ta tasa ma gaba wacce ko yanzu zaune take a d'akinta ta tasa agwalima gaba tana sha yayinda take duba littafan mkrntar ta na boko dana islamiyya , kasancewar yanzu ta gyara d'akinta ta dawo ciki da zama sae bacci ke kaita d'akin inna. Tana cikin duba littanfanta ne taji inna na qwala mata kira taje ta sami inna a falo inna taba ta waya tace"nasiru ne wae ki gaya mae abubuwanda aka ce ku siyo a makrnta. Nan ta kar6i wyr ta snr dashi snn taba inna wayarta ta koma d'aki taci gaba da duba littafanta. Ba ita ta tattara littafan ta ajiye ba sae da ta soma jin bacci duk da cewa dare bai wani yi sosai ba don qarfe tara ne a lokacin. Bathroom ta shiga tayi wanka ta fito tayi shirin bacci cikin riga da wando ta zuba qaton hijabinta ta fito riqe da agwalimar ta guda biyu a hannu. Nan ta had'u da Nasir ya fito d'akin inna zaije d'akinta hannun sa riqe da farar leda mai hoton littafai da kuma al'amin bookshop a rubuce ta gaida shi ya amsa tare da miqa mata ledar yace "duba kiga littafan ne " Ta duba tace "eh sune nagode" Har ya juya zai fita sae kuma ya juyo ya kalleta tayi saurin sadda kanta qasa yace"ki qara hqr kwana biyu kinji ni shiru har yanzu ban sami kaina bane" Tace"ba komai yaya ai ka barshi kawae sae ka sami lokaci" Yace"to sae da safe" Snn ya fita ita kuma taje ta ajiye littafan a d'akinta taje d'akin inna. Da shigarta ta bud'e fridge ta saka agwalimar ta a ciki. Washe gari an sauke Rynt a makaranta sae dube dube take ta inda zata hango mami sbd kwana biyun nn duk suna had'uwa da safe idan an sauke su. Tana cikin dube dube ne sae ga mami ta shigo gate d'in mkrntar da gudu Rynt ta saki murmushi taje ta tarbota tana mae fad'in"wnn gudu haka mami ba kya tsoron kije ki fad'i" Tace"Anti sauri nake kar baki ganni ba ki tafi don na hango lokacinda aka sauke ki mu kuma muna baya da nisa har ma nayi ta kiranki baki ji ba, to kince da nisa ya zan jiki mami, Mami bata ce komai ba sae lunch box d'inta ta ajiye qasa snn ta ciro school bag d'inta dake bayanta ta bud'e ta ciro er wata container rubber mai marfi taba Rynt tace"umma tace na kawo maki" Rynt ta kar6a takai hannu a hnkli ta bud'e. Wacce tana bud'ewa qamshi mai dad'i ya daki hancinta nn taga awara ce wacce taji cabbage da albasa bayan sauce d'in hantar rago da aka zuba akai mai had'e da kayan lambunda aka yanka su slice by slice ta yanda kallo d'aya zakayiwa awarar ka sami kanka da tsinkewar yawu. Cikin nuna jin dad'i ta rufe snn ta kalli mami tace "kice ma mama nagode sosai kinji" Mami tace"yauwa anti nifa har yanzu bamu je kasuwa ba bare naga raqumi ya shiga akurki,idan ma nayiwa umma magana se dariya kawae take min,ta qarashe mgnr ne shaye da toka. Rynt tayi murmushi tace"umma da kanta take miki dariya" Tace"eh mana" To yi hqr jeki kar a fara maku assembly" Daga hk kuwa sukayi wa juna bye bye suka wuce. 10:00pm Man ne zaune kan bed ya rufe laptop d'inshi ya d'aura kan bedside drawer ya kwanta sae ga malika ta shigo d'akin taje ta kwanta kusa dashi had'e da kai hannu tana shafa sajen fuskar shi har izuwa qirjin shi, kallonta yayi tare da janye hannunta daga kan jikinshi ya kashe wuta had'e da juya bayan shi,nn yaji ta matso gab dashi ta rungume shi ta baya yace"pls malika bana son damuwa kin sani,ki matsa kusa dani bana son jinki a bayana. Kmr kazar da qwai ya fashewa ta jaye jikinta daga nashi. Billy Giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 [10:34PM, 2/12/2017] Billy giro😊: ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮``` 🔮🔮🔮🔮 *page* *```50```* Washe gari guraren qarfe goma na safe mohd ne ya fito daga bathroom sanye da white bathrobe wanda kai tsaye gun wardrobe ya nufa ya ciro black suit ya ajiye kan bed yayinda malika ke kwance akan bed d'in tana ta sharar bacci. Bayan ya gama shirin sa tsaf ya d'auki makullin motar sa ya fita,ya bud'e motar sa zai shiga knn sae ga driver yazo byn sun gama gaisawa ne yake cewa "yalla6ai lafiya kwana biyu naga mami da yayarta basa fitowa zuwa mkrnta ko anyi hutu ne banida labari? Ba tare da yako kalle sa ba yace"sunyi tafiya ne" Daga hk kuma ya shigewar sa mota yaja ya tafi. Yana shiga office wayar sa ta shiga ruri ya ciro wyr a aljihu ya d'aga tare da fad'in"Aamil ya akayi ne" Daga d'ayan 6angaren yace"man muna son zamu shigo 9ja ne but no actual time,bcs akwai wani aikin da Amir keson qarasawa da sae idan ya kammala shi ne snn ko zamu zo,but idan mun zo d'in wnn karon ba a gida zamu sauka ba a gidajen mu zamu sauka shine muke son kasa a fara gyara mana gidajen sbd may be gyaran zai d'an d'auki lokaci kan irin yanda aka jima ba'a shiga gidajen ba,if ma gidajen na buqatar canjin komai pls duk kasa canza a mana. Man yace"ok naji ka gaida Amir bye" Daga hk ya katse wayar yaje ya zauna kan kujerar sa mai shillo tare da kai hannu kan landline ya latsa lambobi ya kira, ba jimawa sae ga wata er kyakkyawar farar yarinya ta shigo da bazata wuce 22 yrs ba d'auke da teacup n saucer a hannunta taje kan desk ta ajiye masa snn ta juya ta fita. Mohd dake latse latse da laptop d'insa yakai hannu a hnkli kan teacup d'inda ke kan saucer ya d'auka had'e da kai bakinsa yana shan tean da ke ciki yayinda yake ci gaba da latse latse da d'ayan hannunsa. Malika kuwa tunda ya barta ba ita ta farka ba sae 12 wacce da tashin ta ta fad'a bathroom tayi wanka ta fito taje d'akinta ta shirya kafin take sa cleaner ya gyrawa mohd d'akin shi. Bayan ta gama shiri ne tazo downstairs tayi breakfast taje kan 3seater ta kwanta sae chat take. Sae jin tayi an fizge wyr tayi saurin tashi zaune had'e da kallon wanda ya fizge wyr. Qawar ta Fa'iza ce ta gani tana mata dariya itama dariyar ta mata snn tace"yau kuma bazata kika min" Tace"wlh kedai kan hanya muke nida hubby zamu je gidan su shine nace ya d'an biyo dani nn mu gaisa mun kwana biyu bamu had'u ba tun asibiti" Malika tace"aini fushi ma nake yi dake wae ace tun asibiti ba waya ba text ba chat" Sae da Fa'iza ta nemi guri ta zauna kusa da ita snn tace"wlh banji dad'i bane kwanakin nn shiyasa banida lokacin waya don kashe ta ma nayi sae yau na kunna" Malika tace"eyyah to ya jikin? Allah naji sauqi sosai ya man da haqurin rashin babyn shi da yake fama? Malika tayi er dariya snn tace"in gaya miki har yanzu ya kasa haqura ya cire abun a ranshi har ma baya son damuwa kwata kwata he is so lonely. Fa'iza tace"lallai yana son baby sosai sae ki hanzarta ki samar mai wani " Tace"Hm ba yanzu ba sae mun gama baje soyayyar mu tukun" Fa'iza tace"ta bayan fa da akayi? Aikin san wnn soma ta6i ne ga kuma wnn abar wacce duk da nasan ba kulata yake ba amma idan na tuna cewa wae mtr my man ce sae na nemi farin cikina kaf na rasa but now nsn cewa ni kad'ai ce nayi waje da matsiyaciyar banida wata damuwa sae hln damuwa da my man d'ina yake ciki a yanzu wanda ko shi na d'an kwanaki ne zai ajiye shi mu dawo normal. Fa'iz tace"hkne kam kinga bari na tashi naje nabar hubby shi kad'ai a mota" Nan malika ta tashi taje har mota ta rakata suka gaisa da mijin fa'iza snn ta dawo. Rynt ce a class ita da qawar ta sae er fira suke yayinda Rynt ke d'anyi tana duba littafinta kasancewar free period suke malami ba zai shigo ba. A cikin firar ne qawarta ta riqo hannun Rynt tace"ni kuwa Rynt kinga wani haske da kika soma yi harda er qiba da kuma wani irin laushi da jikin ki ya qara gaya min meye sirrin" Ta qarashe mgnr tana murmushi haka ma Rynt murmushin tayi snn tace"hm yanayi ne kawae....da kuma hutawa ba,cewa da qawarta, Rynt wacce still murmushi nakan fuskarta ta girgiza kanta tace"Sarah knn ba kya rabo da wasa" Sarah tace"Allah ki tambaya kiji duk wanda ya kalli ftr jikin ki yasan cewa ke er hutu ce" Rynt tace"jikin ne kawae" Sarah tace"ba wani nn kedai kawae ba kya son a fad'a ne" Rynt dae bata sake cewa komai ba sae murmushi kawae da tayi yayinda Sarah ta d'aura da cewa keda yayanki skin nature d'inku d'aya sae dai ya fiki kyau da haske" Da wasa Rynt ta bugo ta tace"is not gud mun sami time mu 6ata shi a banza karatu ya kamata muyi ba surutu ba" Sarah tace"to qanwar biro da takarda ke kullum karatu dae karatu ba hutu" Rynt tace"naji dae muyi karatun idan kuma kince srt sae na qara gaba" Ta fad'i hkne had'e da yunqurin tashi Sarah tayi saurin cewa "no yi hqr muyi karatun to" Da haka kuwa kowaccen su ta kama litfafinta suna dubawa yayinda wasu en class d'in keta fmn hayaniyar su har da su tsokane tsokane da guje guje" Can Rynt tayi d'an guntun tsaki ta kàlli sarah tace"Sarah nifa surutun nn ya isheni muje library" Nan kawae sarah ta bud'e tsakiyar littafinta ta 6alli paper tare da bud'e murya tace"noise maker!kuma d'iya ko dogon motsi kikayi wlh sae na rubuta sunanki na kuma had'aki da uncle ci ubaka" Sae kaji take class d'in yayi tsit sbd kowa na tsoron malamin ga kuma Sarah no mercy ce kan shine ma yasa aka bata class monitor. Kan desk Sarah ta hau ta zauna inda take fuskantar kowa ta kalli Rynt tare da d'aga mata gira snn tace"to reader master gareki sae kiyi ta krtn ai ko" Rynt tayi nurmushi had'e da girgiza kanta ta jawo littafinta taci gaba da dubawa. Bayan sati d'aya da faruwar haka. Nasir ne shi da Rynt a office d'in abokin sa fa'iz yayinda fa'iz ke snr da nasir cewa "a gsky idan akace a cire mata cikin nn yanzu ba qarama wahala zata sha ba koma nace zata iya rasa ranta gabad'aya dmn watannin cikin sunyi qanqanta da a cire mata shi yanzu sae dae zuwa nn gaba idan ya qara wasu watanni tukun" Nasir ya sauke numfashi had'e da kallon Rynt da kanta ke qasa yace"kinji abinda yace a cire maki ne ko kuwa? Jiki sanyaye ta d'ago ta kalli nasir tace"Aa a barshi idan ya qara watanin sae a cire" Nan Nasir ya kalli fa'iz wanda ya shiga rubuce rubuce akan takarda da ya gama ya bawa nasir yace"a siya mata wad'an nn magungunan ta riqa sha kafin lokaci yayi" Nasir ya kar6a had'e da yi masa godiya snn suka fita. Bayan sun iso gidan inna ne Rynt ta nufi d'akinta Nasir kuwa ya shiga d'akin inna wacce tana ganin shi ta tarbe shi da fad'in"inace anyi nasara? Nasir yace"anyi nasara inna dmn sam bata fhmci wayo ne ake mata ba" Inna ta washe baki tace"kai Rynh knn akwai quriciya shike nn ta yarda idan ya qara wasu watannin zuvarwa za'ayi" Nasir yayi murmushi yace"to inna kinsan fa qaramar yarinyar ce sosai" Wlh kuwa shiyasa na tausaya mata da cikin nn da ta samu da wuri haka da akayi auren na d'auka ko muhammadu zai yi mata en dibarun su ne har ta kammala karatun ta amma da yake shashashan yaro ne ya d'ura mata ciki ya kuma saki" Nasir yace"ayi ta hqr kawae inna da sannu komai zai wuce" Tace"hkne kam amma ya kake gani idan cikin nn ya tsufa haka zatayi ta zuwa mkrnta d'auke dashi kuwa? Eh to nima abinda nake tunani knn har ma nake d'anyin wata shawara a raina sae dae na gama yanke shawar sae nazo mu tattauna,snn kuma akwae wasu magunguna a hannun Rynt da zata riqa sha. Inna tace"to kaddai wata matsalar aka samu a tare da cikin? Ko d'aya kawae na qarin jini ne da kuma lafiya fa'iz ya rubuta mata shine muka tsaya kan hanya na siyo mata" inna tace"ayyo d'an albarka to sannu da qoqari Allah ya qara maka bud'i da qarfin taimako" Yace"amin snn ya fita. Fitar sa keda wuya sae ga Rynt ta shigo d'akin d'auke da murmushi a fuskarta tace "inna kinga yaya nasir ya saya min agwalima mae yawa daga kawae yaganni ina kallon gurin shine ya tsaya da mota ya saya min" Ta fad'i hakane yayinda ta miqawa inna wata er baqar leda cike da agwalima,inna ta kar6a washe da baki tace"d'an albarka shidae akwài shi da qoqàri ,ai wnn sae ki kwana biyu kina shà" Rynt tayi murmushi tace"inna amma yau zaki sha ko" Inna tace"yo ina na iya da harakar tsami kaiwa baaba hurera dae ko ita zata iya sha" Rynt tayi dariya had'e da fita d'akin wacce tasan ko baaba hurerar basha zatayi ba . Washe gari guraren 11 na safe mohd ne zaune a cikin office d'insa yayinda ya jingina bayan sa akan kujerar da yake zaune idanun sa a lumshe sae juyi yake a hnkli. Knocking akayi had'e da shigowa office d'in ba tare da izini ba hkn yasa mohd yayi saurin bud'e idonsa suka fad'a kan abokin sa jamil wanda ya ta6a samun sa gida da jimawa. Man bai ce dashi komai ba har jamil yaja kujera ya zauna sae a snn yace da shi saukar yaushe? Jamil yace"saukar jiya jiya har ma na had'u da matarka sun fito asibiti ita da Nasir, ya ma sunanta? Man dake jingine yana kallon sa ya lumshe ido had'e da fad'in"Rayyanat" Jamil yace"nyc name,amma kuma wae kana nufin har yanzu baka fara kula yrnyr bane da har za'a d'auketa aje da ita wani asibitin bayan ga ka" Man yace"jamil shin me ya kawo ka office d'ina? Murmushin mamaki jamil yayi snn yace"mugun gaye tambaya ta ma kake, to zo nayi mu gaisa idan kuma zan fita na bar ma office d'in ne to" Man ya d'ago daga jinginen da yake had'e da murmushi yace"wato jamil ka fiye surutu har kazo kan abinda bashi bane" Jamil yace"wane zancen ne nayi da bashi bane na matarka ko kuwa? Shi d'in sbd zancenta yana qara min damuwar da nake ciki da kuma qunci sbd abinda na aikata a gareta tun daga rnr ban qara samun sukuni ba, wlh jamil ban....mts kawai dai barshi zan warware matsalar wa ni kad'ai,jamil ya numfasa yace"mtsw shine matsalar ka wlh me zaka ragu dashi dan ka gaya min matsalar ka mun warwareta a tare,shin ka manta ni sau nawa nake gaya ma tawa matsalar mu kuma zauna mu warwareta nida kai" Man yace"wato Jamil tawa matsalar babba ce dani kaina ban san ta inda zan fara warware matsalar ba. Jamil ya tashi tare da fad'in "olryt shikenan ai sae kayi ta fama da matsalar a ranka har taci ka ta cinye" Nn ya kama hnya ya fita man kuwa sae binsa da ido yayi. Billy Giro😊 adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *