Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, April 3, 2017

Dr Khaleel Complete

adsense here  ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 1..... A hankali yake cin fruit Salad din dake gabansa kansa a sunkuye yana murmushin nan nasa mae kyau da ya kai ga har ana iya ganin dimples dinsa, ya girgixa kai snn ya dago yana kallon matashiyar matar dake xaune kan kujerar dake kallon nasa fuskarta a daure ta kafa masa ido tana kallo, murmushi ya kuma yi mai sauti xae yi magana ta rigasa a fusace tace "ohh ga mahaukaciya na magana ko Khaleel, ni ce ma na xama abun dariyarka knn" ya dan marairaice ya ajiye fork din hannunsa yace "ba hka bane Mum, kiyi hkuri," ya dan shafa kansa da damuwa yace "kinsan komai fa lkci ne mum, kawae su Ummi da Abba sun kasa gane hkn ne, sun ki fahimtar abinda nake nufi am just bored of all dis...." shafa kansa ya kuma yi har lkcn fuskarsa na dauke da damuwa yana kallon Small mum din tasa, sallamar da aka yi yasa duk suka maida hankalinsu ga bakin kofa tare da amsa sallamar, mikewa mum tayi ganin baki tayi da fara'arta tana masu sannu da xuwa suka karaso cikin falon aka shiga gaggaisawa, Khaleel ya mike yana kallon Small mum din tasa yace "to mumy sae na kuma dawowa ko xuwa gobe" tace "a'a ka dae dawo xuwa anjima da daddare bamu gama magana ba" yyi murmushi yace "in'sha Allah mum" bowl din fruit Salad din da ya ci ya dauka xae kai kitchen tace "a'a ka bar shi kawae xa a kwashe" yace "No bari in kai mum" ya nufi kitchen da bowl din ya ajiya snn ya fito yyi ma bakin sallama ya fice daga falon yana kallon agogon hannunsa, gun motarsa ya nufa yana tafe yana satan kallon wata bishiya dake dauke da fararen kujerun roba da table a karkashinta ya ga ko wa inda ya gani daxu gurin suna nan ko sun bar wajen, suna xaune ko har lkcn su biyu kmr ynda ya samesu da ya shigo, sae dae wnn karan ba hira suke ba daya na danna wayarta daya kuma na waya ne, hada ido suka yi da warce ke danna waya don ita ma satan kallon nasa take, ya dauke kansa da sauri, ita ko kallon me wayar tayi tana 'yar dariya tace "dubi gantalalle neman gaisuwata yake" da sauri tayi pretend tace "lahh Ya Khaleel yaushe ka xo" juyawa yyi yana kallonta duk da yasan taga shigowarsa daxu bbu yabo bbu fallasa yace "kin ban sako ne" ta dan yatsine fuska tace "No kawae nayi mamakin ganin ka a gidanmu ne yau, coz ba saba xuwa kayi ba, any way ina yini" ya watsa mata wani mugun kallo ya bude motarsa ya shige yyi horn mai gadi ya bude masa gate ya fice daga gidan, dariya ta saki tana kallon kawarta da ta kasa ci gaba da wayan da take ta rakasa da kallo har ta daina hango motarsa mai gadi ya rufe gate din, can ta maida kallonta ga kawarta dake ta faman dariya ta sauke ajiyar xuciya tace "gaskiya gayen nn ya hadu Meenah, ni dae hka kawae naji yana burgeni," Meenah tayi ma kawarta ta wani irin kallo tace "shi Khaleel din ke burgeki? Tabdi da kinsan halinsa da baxa ki ce komai ba wllh! wnn mugun dan rainin hankalin, ae ni tun da na taso kallon arziki bae taba hada mu ba kin dae ga dan uwana ne, ki bari xan baki lbrin ko waye shi salma, kin taba ganin wani cousin dina ya shigo gidan nn ban gaishesa ba, kuma kin dae san ni da son xumunci Salma, tunda har ki ka ga Khaleel ya shigo gidanmu ban gaida sa ba na dauke kai kiyi shiru kawae" Salma tace "haba abun ya ban mmki wllh, to Allah shi kyauta, ni dae mu shiga ciki in yi ma Momy sallama in kama hanyar gida kafin Mama ta fara kirana" Meenah tace "haba tun da wuri hka, to ki bari bakinta su tafi mana, nasan ba dde wa xa su yi ba" Salma ta harare ta tace "lallai kam da yake ke a gidan ku kike ba shiyasa xaki ce in jira bakin da ban san ranan tafiyarsu ba su wuce" mikewa salma tayi ta nufi cikin gida, Meenah ta mike tana dariya ta bita suka shiga falon a tare. Barkan Ku da Sallah sisterz. [10/14, 3:25 PM] ‪+234 806 484 7850‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 2...... Karfe tara da rabi na dare Khaleel ya gama parkin din motarsa a parkin space din dake cikin gidansu dake G.R.A kaduna, ya bude motar ya fito yana kallon motar dad dinsa ko ba a gaya masa ba yasan ya dawo, ya nufi balconyn da xae sada sa da kofar shiga babban falon gidan, can ciki yyi sallama ya shiga falon ya tarda kanwarsa Rukayya kwance tana kallo, ta mike xaune ganinsa tace "sannu da dawowa ya Khaleel" ba tare da ya kalleta ba yace "sannu" snn ya nufi stairs, dad dinsa suka kusan cin karo da ya ja baya da sauri tare da dan ritsinawa ya gaishesa, bbu yabo bbu fallasa mahaifin nasa ya amsa snn yace "ina nemanka a falona" dad dinsa na fadin hka ya juya ya koma xuwa falonsa, Khaleel ya share wata xufa dake keto masa a goshi ya shafa kansa snn ya shiga haurawa saman a sanyaye, dakin mum dinsa ya nufa tana xaune gefen gadonta tana waya, mai aiki na yayyanka mata fruits a faranti, ya nemi gefenta ya xauna har ta gama, tana kallonsa tace "sae ynxu son" ya dan marairaice mata yace "ummi don Allah ki raka ni gun abba wae yana kirana" tayi masa wani irin kallo tace "sae na raka ka? Ashe ko baxa ka je ba" ya ciro handkerchief ya share fuskarsa bae ce komai ba ya mike ya fita daga dakin ya nufi falon Abbansa, xaune ya tarda Abban nasa yana shan coffee, ya xauna kasan carpet din dake tsakiyar falon ba tare da ya kallesa ba yace "Abba gani"Abban nasa ya ajiya kofin hannunsa yace "ka gama play din hide nd seek din dani Khaleel" Khaleel ya dan yi murmushi ba tare da ya shirya ba yace "wllh ba hka bane Abba aiki ne yyi min yawa a clinic" ummi ce ta turo kofan falon ta shigo, Khaleel yaji ddin ganinta ta nemi gefen mai gidan nata ta xauna. [10/14, 3:26 PM] ‪+234 806 484 7850‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 3..... A hankali Khaleel ya daga kai yana kallon Abbansa ganin shirun yyi yawa, kallonsa ya ga Abba na yi, hkn yasa ya dukar da kansa kuma, Abba ya girgixa kai ya sauke ajiyar xuciya yace "me kke nufi da mu Khaleel?" kasa cewa komai Khaleel yyi har lkcin kansa na kasa, Abba ya maida kallonsa ga TVn dake ta aiki a falon yace "shknn, dat clearly shows dat raina mu kawae kayi, don hka ni na yanke shawarar hada ka da either Meenah ko Maryam, ka je kayi shawara ka xabi daya cikinsu, nd bet me, dat wont take a lng tym, ka tashi ka bamu waje" kasa ko da kwakkwaran Motsi Khaleel yyi daga inda yake a durkushe, komae nasa ya tsaya cak, da kyar ya shiga share xufar dake keto masa a fuska ya daga kai yana kallon Mum dinsa da ko kadan bae ga alaman hkn ya dameta ba, sunayen wa inda Abba ya ambato masa suka shiga yawo a kansa, wae Meenah ko Maryam, ji yyi kmr ya saka ma iyayen nasa kuka, Muryar Abba ya ji a tsakiyar kansa yana cewa "nace ka tashi ka bamu waje" dago kansa yyi da sauri ya marairaice murya yana kallon iyayen nasa yace "don Allah don annabi kayi hkuri Abba wllh ni duk bana son su, na maka alkawarin nn da wata daya kacal xan gabato maku da matar da xan aura plss Abbana consider me, nasan na maku laifi" ya karashe mgnr kmr xae yi kuka, Abba na masa mugun kallo yace "ka raina ma kan ka hankali ba mu ba, common get out my frnd" juyawa yyi da sauri yana kallon Mum dinsa, idonsa ya kada yyi jajur cikin rawan murya ya fara mata mgna "ummi don Allah ki sa baki...." harara ta watsa masa tace "da knn ba ynxu ba" dafe kansa yyi xuciyarsa na tafarfasa, ae shi da ya aure wa in nan yaran da abba ya ambato masa gwara ya mutu ba aure, dat aside ma shi ko kadan bae son auren xumunci kallon arxiki baya hada sa da yaran yan uwan iyayensa gaba daya duk baya sake masu, goge Fuskarsa yyi da handkerchief a nutse yana kallon Abbansa ya fara magana "Abba i knw na maku laifi, plss ku yi hkuri ku yafe min, na kuma maku alkawarin nan da wata daya xan....." tsawa Abba ya daka masa yace "Enough Malam, tashi ka ban waje" Khaleel bae kuma cewa komai ba ya mike da kyar ya juya ya fice daga falon. Karfe sha daya da rabi Ummi ta shigo dakin Khaleel, yana kwance ya kafa ma Ac ido da ganinsa kasan abun duniya ya ishesa, ummi ta karaso ta xauna gefensa tana kallonsa ya mike xaune yace "ummina kin ga abinda Abba ke shirin min ko" Ummi tace "to ae kai ka ja ma kan ka Khaleel, tun yaushe muke bin ka kana kakkaucewa ka maida mu yara" komawa yyi ya kwanta bae kuma cewa komai ba, sarai tasan halin dan nata da abun da ke iya faruwa kafin gobe in ya kwana cikin tashin hankalin nn da yake ciki, hkn yasa tace "ka kwantar da hankalinka son, na shawo mana kan Abba amma fa da kyar, ya kuma baka wata dayan da kace don hka kafin lkcn ka gabato matar, kar ka kuma ban kunya kasan ni bana son abinda xae taba min kai son" mikewa Khaleel yyi ya rungume ummin tasa cike da jin ddi ya shiga mata godiya, ta shafa kansa tana murmushi ta sa masa albarka snn ta mike yyi mata sae da safe ta fita xuwa dakinta. Kasa bacci Khaleel yyi daren ranan duk da hankalinsa ya kwanta, amma damuwarsa daya ta inda xae fara nemo matar da xae gabato ma parent dinsa ynxu, ta ina xae fara wnn jan aikin, tunanin hkn na mugun tada masa hankali. [10/14, 3:26 PM] ‪+234 806 484 7850‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 4..... . A hanxarce Khaleel ya gama shirinsa cikin bakar suit da wando da farar T-Shirt sae neck tie ash colour, dakin Umminsa ya nufa ya sameta xaune gaban madubi tana gyara gashinta, yace "ummina xan tafi" Ummi na kallonsa tace "baka yi breakfast ba" ya kalli agogon hannunsa yace "idan naje office xan yi ummi, sae na fara xuwa cikin gari an duba min motata" Ummi tace "ba john ya kai shekaranjiya an gyara ba" ya girgixa mata kai yace "a'a it's still nt ok, xan je da kaina ynxu" Ummi tace "ikon Allah, to shi kadae ne motar ka Khaleel ka dauki wata mana in ya so ko anjima sae john ya maidata" yace "No xan tafi da ita ynxu Ummi na fi son in je da kai na" Ummi tace "to Allah ya tsare" ya nufi kofa xae fita yace "Ameen ummina sae na dawo" tace "to a dawo lfya" a stairs suka hadu da Rukayya tace "yaya baka yi breakfast ba" yace "eh sauri nake sae na je office" tace "to yaya ka ajiye ni ni ma sch xan tafi ynxu" yace "cikin gari na nufa ynxu" yana kai wa nn ya sauka ya nufi kofar fita daga falon, ta bi sa da kallo snn ta dan tabe baki ta nufi dakin ummi. Karfe takwas da kusan rabi Khaleel ya iso cikin gari, ya mika ma engineers din motarsa snn ya nemi kujerah ya xauna tare da fiddo wayarsa yana dannawa to while away time. Tafe take tana bincike jakar dake sakale a kafadarta alaman tana neman abu, cak ta tsaya ta wara ido hade da bude baki ta saki salati tana kallon cikin jakar, hkn ya ja hankalin Khaleel dake xaune har lkcn yana danna waya, juyawa tayi ta bi layin da ta fito daga da kallo, can ta dan tabe baki hade da tsaki ta xuge jakar ta kuma sakala sa a kafadarta da kyau snn ta ci gaba da tafiyarta da takunta mai jan hankali, sanye take da riga da skirt ta atamfa orange colour mae ratsin ash da brown, hijabin jikinta ma orange ne ya wuce gwiwa da kadan, hka ma takalmin kafarta orange ne, jakar hannunta kadae ne brown, da ganinta kasan makaranta xa ta, Khaleel ya bi ta da kallo har ta isa bakin titi snn yyi tsaki ya ci gaba da duba wayarsa, tsaye tayi bakin titin alamar tana jiran abun hawa, ba a Kuma dau lkci ba ta samu ta hau suka bar gurin, kmr ance Khaleel ya juya ya ga wasu fararen takardu a kasa dai dai inda ta tsaya, ya mike ya nufi gurin ya duka ya kwashe takardun har uku yana kallonsu, reciept ya gani da admission letter sae handout na physics, ya girgixa kai hade da tsaki da kmr xae wurgar da su sae kuma ya fasa ya linkesu ya koma ya xauna da xumar ya ba kanikawan idan sun ganta su bata, cikin minti sha biyar aka gama yi ma motarsa abinda ya kamata, ya basu kudi duk da basu bukaci hkn ba snn ya shige motarsa ya kama hanyar office cikin hanxari don ya makara. Tana xaune a class ta sa Chemistry text buk dinta a gaba kmr me karatu taji an rankwasheta, ta juya da sauri kuma a fusace don taga waye, ta wani hade rae tace "bana son irin wasan nn Aisha" Aisha ta xauna tace "Allah ya baki hkuri" sauran kawayen nata ma xaunawa suka yi suna kallonta, Ummi tace "wae me ya faru ne Ashnaah yau duk you re nt ur self" tayi masu wani irin kallo tace "dole ku ce am nt my self tunda ba reciept dinku bane ya fadi" Maryam tace "au wae shi yasa kika xama hka, ba mun ce maki xaki gani ba kila ma a gida kika xubar" tsaki Ashnaah tayi tace "eh naji xan gani a gida ku rabu dani" Bilkisu ta mike ta bar wajen Nafisa ta bi bayanta, Ashnaah ta bi su da harara, snn tace "bari in ta murna na xubar da reciept dina" tana kai wa nn ta mike ita ma ta fice daga class din, Ummi tace "da'alla mu rabu da ita mu muka xubar mata" mikewa su ma suka yi suka bar class din. [10/14, 3:26 PM] ‪+234 806 484 7850‬: ~Dr Khaleel By Khaleesat Haiydar 5..... Khaleel ne xaune office dinsa ya jinginar da kansa jikin kujera idonsa lumshe, maganganun umminsa ne ke masa yawo a ka, tunanin ta Inda xae fara neman mata kawae yake, ko kadan shi kam matan kaduna ba su masa ba, basa burgesa, bude office dinsa da aka yi ya sa ya gyara xamansa da sauri ya bude ido ya ga wani isasshen ne xae shigo masa office ba knocking, ta rufe kofar bayan ta shigo, ya wani hade rae yana kallonta, da ma yasan baxae wuce ita ba, bae jira jin me xata ce ba a nutse yace "get out" ta dan marairaice masa tace "ka ga fa files na kawo maka Sir" ya kuma hade rae yace "ki bar min office nace" ajiye files din hannunta tayi nn da nn idonta ya kada, ta juya xata fita, murya can kasa yace "Ameesha" ta juya tana kallonsa sae ga hawaye, ya mike tsaye ya karasa kusa da ita ya kamo hannunta, sae ta sakar masa kuka, dafa kafadarta yyi ya dago kanta yana goge mata hawayen idonta a hankali yace "am sorry" gyada masa kai tayi hawaye na ci gaba da xuba a fuskarta tace "Abbana yace in kawo maka files" tana fadin haka ta juya ta Fita daga office din tare da kullo masa kofarsa, komawa yyi ya xauna ya lumshe idonsa duk abun duniya sun ishesa. Bayan minti goma da fitan Ameesha aka kwankwasa masa kofa, ya tura file din gabansa bayan kmr minti daya yace "come in" wata nurse ta shigo rike da file a hannunta ta gaishesa cike da ladabi snn tace "Dr patient xaka duba, kuma Emergency ne, yace "don me xaki kawo min baki kai ma Dr Umar ba, ni din engine ne?" Tace "No sir suna Theatre ne, Oga ne yace in kawo maka" tsaki yyi ta ajiye masa file din ta Fita, ba a dau lkci ba nurse din ta dawo da patient din ya daga kai yana kallon yarinyar da baxa ta wuce sha takwas ba, bbu abinda take sae kuka tana rike da cikinta, ya dan yi tsaki Mara sauti ya jawo file dinta ya bude yana dubawa, nurse din ta juya ta Fita, yace "ke malama ba kuka xa ki min ba amsa min duk tambayoyina xa ki," shiru tayi tana goge hawayen fuskarta tana kallonsa, jin ynda tayi shiru lkci daya yasa ya daga kai yana kallonta, ta sunkuyar da kanta da sauri, cire farin glass din idonsa yyi ya sake fuska ya dan sassauta murya yace "daurewa xa ki yi Zeenat and tel me wat ur prblm, look at me" ta daga idonta da ya rine don kuka tana kallonsa, ya sakar mata murmushi snn ya shiga yi mata tambayoyi tana basa amsa. Karfe hudu da rabi Ashnaah ta shigo gida ta jefar da Jakarta nan bakin kofa ba tare da ta kalli inna dake tuka tuwo tsakar gidan ba ta Shige falo, inna ta tabe baki tace "aniyar ki ta bi ki yarinya, kuma ba ni kika wurga ma jaka ba, Adamu kika jefa ma" Ashnaah ta fito tace "kin fara ko inna ni dae fa ki dinga kyaleni, kina ganin na batar da takardun makaranta na gaba daya duk ban gani ba" inna ta mike da sauri ta dafe kirjinta tace "takardun makarantar ki?" Ashnaah kmr xata yi kuka tace "eh mana" inna tace "barawo ne ya sace su ko ya aka yi?" Ashnaah tace "eh mana, kuma gashi ni ynxu bn san me xan ce a makaranta ba, ga kuma Abba ma ban san me xan ce masa ba" inna tace "to wa ke ta wani Abba can, ynxu kawae gobe in shirya in rakaki makarantar in yi ma masu makarantar bayani," Ashnaah ta xaro ido ta kwashe da dariya tace "Allah ya tsareni, ance maki makarantar ta yara ce kuma snn ba a bari tsofaffi su shiga, ynxu dae abinda nake so dake kawae ke ce xaki ce ma Abba kina kwalema sae kika bude jakar makaranta ta kiga takardu sun yi yawa sae kika kwashe kika xubar kuma masu kwasan shara suka xo suka xubar kinga ae baxae iya cewa komae ba sae ya tafi makaranta yasa a min sabo," inna tace "ae wnn abu me sauki ne Allah ya kawo sa" Ashnaah tayi murmushi tace "shi yasa nake son ki inna." [10/14, 3:26 PM] ‪+234 806 484 7850‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 6..... Khaleel ya ajiye pen din hannunsa yana kallon mahaifin Zeenah dake xaune gabansa yace "ka kwantar da hankalin ka sir, in'sha Allah ur dota will b alryt but nt until yhu give her wat her heart desires" Alhajin yace "nt at all, ni ban tada hankali na ba ae, just dat aure ne dae sae na mata ko ta ki ko ta so, sae dae in mutuwa tayi" Khaleel yyi shiru yana kallonsa, can dae yace "duk da halin da take cikin ynxu Alhaji" Alhajin yace "kwarae kuwa" yana kai wa nn ya mike ya fice yana cewa "to in ta mutun ma uwarta dake xugata tayi asara ba ni ba" Murmushi Khaleel yyi ya daga kafada ya ci gaba da abinda yake. Karfe shidda saura na yamma Khaleel ya rufe office dinsa rike da suit dinsa ya nufi ward din da patient din tasa take, tana xaune tayi jigum, wata matashiyar mata na yanka mata fruit ya karaso cikin dakin yana kallonta yace ya jikin?" Kai kawae ta gyada masa, matar dake yanka mata fruits tace "sae dae fa kirjin nn tace bae daina ba, kan ma ynxu take ce min ya fara mata ciwo," yace "ae dama ba lkci daya ciwon kirjin xae daina ba, anjima xa a shigo mata allura a kuma bata drugs, Allah ya sauwake" yana kai wa nn ya fice daga dakin, last floor ya haura ya nufi wani office, ya kwankwasa kofa aka masa ixinin shigo wa ya bude kofar ya shiga da sallamarsa, yana xaune kan daya daga lafiyayyun kujerun office dinsa rike da jarida a hannu, Ameesha kuma na xaune kan office chair dinsa tana danna laptop, Khaleel ya gaishesa cike da ladabi, ya amsa tare da cewa "yhu re off knn" Khaleel yace "eh dad amma kila in dawo can da daddare," juyawa yyi yana kallon Ameesha yace "baki tafi gida ba dama" Ameesha ta rufe laptop din gabanta tace "dama kai nake jira Dr, drop me" Dakewa Khaleel yyi tare da kirkiro murmushi yace "ni cikin gari na nufa ynxu driver ya kai ki kawae" kmr xatayi kuka tace "plss mana" bata jira me xae ce ba ta mike da sauri ta dauki dan farin mayafinta tayi roll dinsa kan farin uniform din jikinta snn ta figi Jakarta ta dauki laptop dinta tace 'bye dad sae ka dawo" Abban nata yace "yau dae ba aiki kika xo yi ba pretty," juyawa Khaleel yyi ran sa a bace ya fice daga office din, yana gaba tana biye da shi a baya da sauri yake tafiyar tasa, hkn yasa ta kirasa kmr xata yi kuka, ya xabga mata wani mugun harara ya karasa parking space Inda motar sa yake, Sosae jikinta yyi sanyi ta shiga binsa a sanyaye, yana isa gun motar sa ya saka hannu xae Ciro makullin mota a aljihu yaji takardu, fito dasu yyi yana kallo da dan mamaki sae a snn ya tunasu receipt din daxu da ya tsinta, yyi tsaki ya cukuikuye su ya jefar, Ameesha da ke tsaye dan nesa da shi tace "kasan me ya Khaleel, na manta xan tafi gun frnd dita ka tafi kawae" tana kai wa nn ta juya da sauri ta nufi gate, ya bita da kallo snn ya kauda kansa ya bude motarsa xae shiga idonsa ya sauka kan takardun da ya jefar, karasawa yyi ya duka ya kwashi takardun kuma snn ya shiga motarsa ya tada ya fice daga asibitin bayan an bude masa gate, a hankali yake tukin har ya iso Ameesha dake tsaye bakin titi tana jiran abun hawa yyi parking ya xuge glass yace "shigo mu je" xata yi magana ya daura yatsunsa kan lips dinsa alamar kar tace komae, a hankali ta bude motar ta shiga ya ja motar suka bar wajen. [10/14, 3:26 PM] ‪+234 806 484 7850‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 7..... Karfe hudu saura na yamma Khaleel yyi parking motarsa dae dae gun da aka masa gyara jiya da safe, masu gyaran motar suka karaso ya fito suka gaisa suna tambayarsa ko gyaran ne bae yi ba still, Khaleel ya fito da takardun hannunsa xae yi magana knn ya hangota ta fito daga wani mota da yyi parkin gefen titi, tana gyara mayafin dake kafadarta rike da jakarta ta kulle kofar motan, kallonta kawae Khaleel yake ko kiftawa baya yi, wani hadadden guy ne ya fito daga bangaren maxaunin driver, ita ko tuni ta fara tafiya saman layin, sunanta ya shiga kira ta juya a dan fusace tace "don Allah kar ka jawo min attention nn ni dae, nace maka sae gobe" tana kae wa nn ta yi gaba, yyi murmushi yana shafa sajensa, Khaleel yyi tsaki ya juya yana kallon kanikawan dake jiran jin me ya kawo sa yace "xan dawo gobe ma dae" yana kai wa nn ya shige motarsa ya bar gun. Ashnaah ta gama fesa turarenta na biyar snn ta dauki mayafinta ta yafa ta juya tana kallon inna da ta saki baki tana kallonta tace "inna gidan kawata xan tafi ynxu, ko da Allah xae kawo Abba kar fa kice masa na dawo daga sch fa" inna tace "to da magariban nn xaki gidan kawa Takwara" Ashnaah ta hade rae tace "karfe biyar ne magariba inna, ni dae na tafi ba dde wa xan yi ba" tana kai wa nn ta fice, dae dae bakin kofa suka ci karo da Abbanta, gabanta yyi mugun faduwa yana kallonta yace "ina xa ki?" Ta fara Kame kame, ya daka mata tsawa ta juya ta koma ciki da sauri, Abba ya shigo falon yana mata mugun kallo yace "wa ke dawo dake gida kusan kullum a mota Fateemah?" Ta tsorata ssae cikin rawan murya tace "ni Abba?" Inna ta mike tsaye a fusace tace wani munafukin ya gaya maka hka, ohh jita jitan Mara su aikin yin yan unguwan nn xaka dauka ko, to ko ma wani magulmacin ya gaya maka ka koma kace masa baxae taba albarka ba a rayuwa indae har jikata xae kafa ma ido." Abba ya kirgo dubu goma ya ajiye mata yace " ni xuwa gobe xan tafi Abuja kila inyi wata daya ko ma fin hka" ya juya yana kallon Ashnaah yace "ki same ni gida anjima" yana kai wa nn yyi ma mahaifiyarsa sallama ya fice, Ashnaah ta fashe da kuka ta xube kasa, inna tace "meye abin kuka, ae bbu Inda xa ki," Ashnaah ta mike tana ci gaba da rusa kuka ta shige daki. Washegari da sassafe Ashnaah ta gama shirin makaranta ta bar gida, sae da ta fara biyawa gidan Abbanta don amsa kiran sa, yana breakfast ta shigo gidan, hkn yasa ta nufi dakin momynta, ta sameta xaune ta gaisheta, bbu yabo bbu fallasa ta amsa, Khadija ce ta shigo dakin da shirin makaranta ta ce "lah Ashnaah yaushe kika xo?" Ashnaah tace ynxu, Khadija tace "Mami ni xan tafi" Ashnaah tace "jirani mu Fita tare" Abba na gama break fst Ashnaah ta tafi falo tare da Khadija, Abba na rufe jakar laptop dinsa da xae yi tafiya da, Khadija ya kalla yace je kira min Mamarku, ta juya ta koma sama suka sakko tare da ita, suka shigo falon suka xauna, tuni gaban Ashnaah ya fara bugawa don bata san me Abbanta xae gaya mata ba, dama kullum ita cikin laifi take gashi an samu Wanda ya kuma kawo masa gulmanta, ta juya ta kalli 'yar uwarta dake kallonta ta galla mata Harara ta dauke kanta. [10/14, 3:26 PM] ‪+234 806 484 7850‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 8..... Kujera ya ja kusa da gadon da take kai ya xauna yana kallonta, hawayen da ya ki tsaya mata kawae take share wa, yace "to ki bani dalilin da yasa baki son Wanda ake son hada ki da," da kmr baxata ce masa komae ba sae kuma ta tsayar da kukan da take murya can kasa tace "sbda nasan ba sbda Allah yake so na ba," Khaleel ya kau da kai yana murmushi yace "to sbda me yake son ki" kin cewa komae tayi sae wani sabon hawayen da ta shiga yi, yace "ki daina stressin kan ki da kuka" bata ce komae ba sae kokarin daina kukan da tayi, yana kallonta yace "yaushe ne bikin naku?" A raunane tace "saura sati uku" Khaleel yyi shiru yana kallonta snn yace "amma mijin naki ya xo duba ki kuwa?" Cikin kuka tace "ni ba mijina bne kuma ban gansa ba wae yana Egypt" Khaleel xae yi magana aka bude kofa Ameesha ta shigo rike da faranti silver Mae dauke da allurori da wasu magunguna, da fara'arta t karaso kusa da gadon tana cewa "ya jikin Zeenah?" Zeenah ta dan yi murmushi tace "da sauki" ko kadan Ameesha bata lura da cewa Khaleel bane xaune kusa da ita don yyi backin kofar ne, ya juya yana kallonta yace "Ashe baki tafi ba" da sauri Ameesha ta juya tana kallon Inda yake da mamaki, juyawa tayi tana kallon Zeenah, snn ta kuma kallonsa, kirkiran murmushi kawae tayi tace "uhm ban tafi ba," tana kai wa nn ta ajiye farantin hannunta ta juya ta fice da sauri, Khaleel ya bi ta da kallo, snn ya ci gaba da yi ma Zeenah tambayoyin da yake mata, ba shi ya bar dakin ba sae kusan karfe shidda na yamma bayan ya kira wata nurse ta yi mata alluran da Ameesha ta shigo da ta bata magungunan ma. Khaleel na Fita haraban asibitin ya ga motar Ameesha, duk a tunaninsa wucewa tayi, yyi tsaki a xuciyarsa yace kin gamu da wahala yarinya ko kadan mata marasu class basa burgesa gashi har yau bae hadu da mace mai class irin Nasa ba, gun motarsa ya nufa ya bude ya shiga ya tada ya bar asibitin. Sae dae ya fara yin maghrib a hanya snn ya iso gida, bbu kowa falonsu sae TV dake aiki, ya na haurawa sama suka kusan cin karo da Meenah tayi baya da sauri ta bi gefensa xata wuce ya fixgota yace "me ya kawo ki gidan nn" duk da ta tsorata amma bata nuna masa ba ta dake tace "wnn kuma naga ae ba matsalarka bace ya Khaleel" matse ta yyi a bango tayi yar kara hkn yasa ya saketa da sauri ya buge mata baki snn ya shige dakinsa, tace "Allah ya Isar min, mugu kawae" tana kai wa nn ta sauka kasa da sauri. Khaleel na kwance dakin mum dinsa da daddare, tace dama ina son muyi wata magana Khaleel, Khaleel ya Mike xaune yace " ina ji Ummi," sae da ta gama abinda take snn ta juya tana kallonsa tace "kan Ameesha ce Khaleel, kai ma kan ka kasan irin son da take maka ba sae na gaya maka ba dae ko" nn da nn Khaleel ya hade rae yana kallonta yace "so na kuma Ummi," ta hararesa snn ta ci gaba da maganarta,"daxu ta xo ta same ni tana kuka......" Mikewa Khaleel yyi ransa a bace yace "tace miki me Ummi, ni fa wllh bana sonta, bata kuma kai matsayin in so ta ba, me xanyi da macen da bata da aji" yana kai wa nn yace sae da safe Ummi, snn ya fice daga dakin. Yana komawa daki ya shiga Neman layinta ransa a bace amma duk bae samu ba, hkn ya kuma bata masa rae, kulle dakinsa yyi da makulli snn ya dauki makullin fridge dinsa ya bude ya Ciro wine ya xuba a cup ya shanye nn take,sae da yyi hkn kusan sauri uku snn ya fada kan gado yyi ruf da ciki ya lumshe ido, mikewa yyi bayan kmr minti biyar ganin bacci na son daukesa ya shiga bayi ya wanke bakin sa snn ya fito ya isa kusa da bedside lamp xae kashe ya ga takardun da ya ajiye tun shekaranjiya a gurin, dauka yyi yana kallonsu, lkci daya fuskar Ashnaah ta dawo masa, xaunawa yyi yana rewinding din abinda ya gani shekaranjiya, wallet dinsa ya dauka ya linkesu ya saka su ciki don kar ya manta gobe. Washegari karfe biyu da rabi ya bar office ya nufi cikin gari, ba gun masu gyaran mota ba yyi parkin dis tym around, gama parkin dinsa ke da wuya ya Hangota tana fitowa daga layin nasu da hijab dinta har kasa, fitowa yyi daga motar ya tsaya dai dai inda yasan xata bi har ta karaso snn yace "Hey minti biyu" juyawa tayi da dara daran idonta tana kallonsa, shi ko ya hade rae don tunda yake bae taba tsayar da mace ba, kai hasali ma bae taba fara yi ma macen da bae sani ba mgna, ta wani hade rae tana masa mugun kallo daga sama xuwa kasa tace "da wa kke" [10/14, 3:26 PM] ‪+234 806 484 7850‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 9..... Da mamaki Khaleel ke kallonta, ya karyar da kai yana mata wani irin kallo yana nuna ta yace "da wnn abun nake" wani matsiyacin kallo tayi masa ta ja tsaki tace "kan ka ake ji" xata canxa hanya ya kuma shan gabanta, a fusace tace "dalla Malam ka bani hanya in wuce ko kana hauka ne" ya wara ido yace "ni din ke hauka," tsaki tayi ta juya a fusace xata koma Inda ta fito ya fixgota da karfi yace "ni kika ce ma mahaukaci?" Bae rufe baki ba ta sauke masa mari, ya sake ta a hankali yana kallonta da mugun mamaki, tuni kallo ya dawo Kansu, tana hararansa tace "kadan ka gani" juyawa tayi abunta da sauri ta bar gun ta koma gida. A fusace ta shigo gida ta cire hijab din jikinta ta jefar kan kujera, inna tace "me ya faru kuma" labarta ma inna abun da ya faru tayi inna tace "kin min dae dae da hudu kika yi masa Marin ma" a guje Khaleel ya shigo compound dinsu da motarsa ya bar sa nn tsakiyar gidan ya fito ya rufe motar ba tare da ya sa mata key ba ya shige gida, dakinsa ya nufa ya fada kan gado yyi rub da ciki ya rumtse ido xuciyarsa na ci gaba da tafarfasa, bayan minti goma da shigowarsa aka bude kofar dakin a hankali, ya bude idonsa da sauri ya juya don ganin wnda ya shigo masa, Ameesha ce ta shigo dakin da sallamarta ya Mike tsaye da sauri ya karasa Inda take ya fixgota a fusace yace "wae ke me ke kawo ki gidanmu" a dan tsorace tace "ni gun Ummi nake xuwa ya Khaleel," Mari ya xabga mata yana huci yace "kike ce mata me?" Bae jira me xata ce masa ba ya tura ta da karfi, ya nufi bathroom, sae a snn ya ji sanyi a ransa, xuciyarsa ya daina masa xugin da yake masa da, shower ya sakar ma kansa a bathroom, bayan minti kusan ashirin ya fito yana goge gashin kansa da towel ya xauna kan gado fuskar nn tasa bbu annuri, ya bude fridge dinsa ya Ciro wine dinsa ya kulle kofar dakinsa snn ya kafa kwalban a baki, sae da ya kusan shanyewa snn ya ajiye kwalban ya dafe kansa, ya kai minti goma a hka snn ya juya ya fada kan gado sae bacci. Ba shi ya tashi ba sae kusan magrib, shima Ummi ce ke ta buga masa kofa tana kiran sunansa, ya mike xaune yana kallon agogo, tashi yyi ya dauke kwalban wine din da yasha ya mayar cikin fridge snn ya bude mata kofar. Karfe takwas da kusan rabi Khaleel ya sakko downstairs sanye da jallabiya milk colour yana rike da makullin motarsa ya karaso cikin falo yace ma Ummi dake binsa da kallo "xan je gidan su Ameesha Ummi sae na dawo" tayi masa Allah ya kiyaye snn ya Fita. Tuki yake amma bbu abinda ke masa yawo a kai sae abinda ya faru daxu, yyi murmushin mugunta yana shafa sajensa yace "Amazing" Mai gadi ya sa yyi masa sallama da Ameesha, duk da ya shiga compound din nasu, mai gadin ya dawo yace ya bada sakon, horn aka yi mai gadi ya bude da sauri sae ga Mahaifin Ameesha ya shigo, Khaleel bae ji ddin hkn ba, amma dae ya fito suka gaisa da Boss din nasa, Alhajin yace "ya baka shiga ba Khaleel sae kace wani bako" Khaleel yyi murmushi yace "ae tana fitowa Abba" komawa yyi cikin mota bayan wucewar aminin dad din nasa, amma wnn karan back seat ya shiga, a hankali take tafiyar har ta karaso gun motar snn ta tsaya, ya bude motar yana kallonta ta dauke kai, da gninta kasan ta ci kuka, wayarsa ya shiga ring ya duba ya ga Abbanta ke kiransa, ya daga, Abban nata yace"khaleel ka dan je clinic ka dauko mata magani don Allah wae cikinta ke ciwo." Khaleel ya kuma kallonta snn yace "to Abba." Ya kashe wayar. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 10..... Shiru Zeenat tayi tana kallon Khaleel a dan tsorace, yace "yes dats d only way out, in ba dae ki fito da wanda kike so ba sae in san ynda xanyi convincing din dad dinki ya fasa hada ki da wanda ba kya so din ba" A sanyaye tace "to doctor Momy na fa ni dae ina sonta ssae" yace "daga baya we let her knw everythin" Zeenat na share hawayenta tace "am greatful doctor" yace "Neva mind" snn ya fice daga ward din ta bisa da kallo, Allah kadae yasan abinda take kitsawa a xuciyarta, shigowar kannin mum dinta ne ya dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi, ta sakar masu murmushi suka ce to ki tashi gimbiya an sallamemu, wanda ya shigo bayansu yasa ta hade rae, ya karaso kusa da ita da damuwa yace "sannu prettyna an sallame mu" harara ta galla masa ta mike da sauri ganin yana kkrin daga ta, ta figi hijab din ta tasa ta bi bayan wasu daga kannin mum dinta da suka fita da kayayyaki hannunsu, harabar hospital suka yi ido hudu da Khaleel dake xaune kan farar kujerar roba da wani frnd dinsa, Zeenat ta sunkuyar da kanta, Khaleel ya bi gayen da Zeenat tace shine wanda ake son hadata da kallo, yyi murmushi, yan uwanta suka yi masa sallama da godiya snn suka nufi parkin space inda motarsu yake, bin Zeenah yyi da kallo har ta isa gun mota, abokinsa na dariya yace "kai wnn kallo hka Khaleel, habit din nn naka dae baka bar shi totally ba knn" Khaleel yyi murmushi yana shafa sajensa yace "yarinyar tayi ne, ga ta doguwa ga shape ga diri, ga ga... Infact komai yaji" sae kuma ya tabe baki yana girgixa kai yace "amma sae dae baka ce" dariya abokinsa ya dinga yi yace "I knw yhu can Neva Change from hu I knw yhu Khaleel" Khaleel ya mike yana yar dariya yace "wllh Khaleel ya canxa" abokinsa ya rikosa yace "wait Khaleel wae ya maganar auren ka? Ka samu mata kuwa? Khaleel ya koma ya xauna yace " ina fa, frnd na rasa ynda xanyi da parent dina" frnd din nasa yace "to ko baturiya kke son aura" Khaleel yace "ae baxa su bar ni ba, amma hkn bayi niyya da" abokin yace "to wae in tambayeka mana Ameesha fa, naga she is very beautiful, educated, in fact...." Katse sa Khaleel yyi a fusace yace to kai ka aureta mana, Allah ya tsareni auren macen da bata da class" Abokinsa yace amma ka mata shaidar karya, yarinya da ko kallon namiji bata yi amma don tana sonka sae kace bata da aji," Khaleel ya mike yace "kaga ni na koma office" yana kai wa nn yyi gaba. Khaleel ne xaune ran Sunday da frnd dinsa a gidan wani abokinsu, ya Kai karshen lbrinsa yana murmushi ya dauki kwalban wine din gabansa yana sha, duk suka yi tsit suna kallonsa kowa da mamaki bayyane a fuskarsa, mikewa Najeeb yyi yana tabe baki yace "amma ka bada maxa Khaleel, na sha surprise dinka, duk wnn ajin naka da Kyan ka, da kudin ka da iliminka da wayewar ka mace ta mare ka ka kyaleta??? Yhu let her go scot free? Just like dat" murmushi kawae Khaleel yake, duk abokan nasa suka masa caa da surutu ko wannensu rae a bace" sae da ya bari suka yi shiru don Kansu snn yace "nima har kun bata min rae tunda kuka iya mance wanene Khaleel, an gaya maku Khaleel xata Mara ta tafi scot free" Abdul ya mike yace "nonsense, after she've disgraced yhu in public and yhu let her go, me kuma kke tunanin xaka mata da xa ka burge?" Dariya duk frnds dinsa suka dinga yi, ya daga kai yana kallonsu yace ae abinda xan mata sae ya sa ta yi da ta sanin haifota da uwarta tayi duniya, ni ina da reason dina na kyaleta. Najeeb ya bushe da dariya yana nunasa yace "ya wuce kace xaka yi rapin dinta ko kuma ka sa a xuba mata acid, ko a nakasata, kai dae nasan baka kisa, dats d only thin yhu can do, nothing more then dat, kuma still baka burge mu ba, yarinya ta sa hannu ta sharara maka mari ka bar ta ta wuce baka babbala bnxa ba mu ga wanda ya tsaya mata, nayi mmkin canxawar ka lkci daya, ni kam bn ji ddin dawowarka Nigeria ba Khaleel, kawae an bata maka rayuwa ne, iyayenka basu maka adalci ba." Dariya kawae Khaleel yake yana rike da kansa, ya mike yana kallonsu yace "da kun san abinda na tanadar ma yarinyar nn ko, da ta Baku tausayi" yana kai wa nn ya mike ya fice daga falon rike da makullin motarsa. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 11.. Shiru yyi yana kallon small mum dinsa da ta bude baki da mamaki tana kallon sa, can tace "lallai ma Khaleel, sae yau nasan baka da tunani kasan hukuncin abinda kke shirin yi kuwa" Khaleel yace "bbu wani hukunci mum, Kinsan abinda ke iya faruwa da yarinya nn idan ban yi hka ba" Tace "to ina ruwan ka, ka fi iyayenta sanin abinda su ke yi ne" Khaleel ya sassauta murya yace"don Allah mum ki fahimce ni, wllh in kin ga yarinya nn sae ta ba ki tausayi, mu hadu mu ceci rayuwarta plss" da kyar Khaleel ya shawo kan ta, can bayan dan shirun da tayi tace "to shkkn amma ni dae ba ruwana" yyi dariya yace "dama mana, ruwana kadae ne ki kwantar da hankalin ki mum," tace "Atoh" sallama ya mata yace da yamma xae dawo snn ya bar gidan. Ashnaah na xaune a aji da frnds dinta bayan sun gama lecture tana basu lbrin abinda ya faru shekaranjiya tsakaninta da Khaleel, duk suka tsaya kallonta baki bude, Maryam tace "kika maresa Ashnaah?" Ashnaah tayi yar dariya tace "kuna mamaki ne, dan dae hannu baya magana ne da ya Baku lbri" duk suka kwashe da dariya amma bnda Nafeesa da tace "to ki dae bi a hnkli, don in kin mari wani kin xauna lfya to wani ba kyaleki xae yi ba," Ummi tace "to wnn din ma ca yyi maku kyaleta yyi, ba dae ya ga layinsu ba kawae dae Allah ya tsare" Ashnaah tace "to uban me xae iya min? In Baku da abin fadi kuyi shiru pls kar Ku bata min rae, ya dde bae min abinda xae yi ba" Duk suka yi shiru Nafeesa ta mike tace "ki dae bi a hankali" tana kae wa nn ta fice, Ashnaah ta bi ta da masifa wae aniyarta ya bita, canxa hira kawayen nata suka yi, Maryam tace " wae ina saurayin nn naki me kawo ki makaranta Ashnaah" Ashnaah tace "uhn ki bari kawae akwae abokan babana masu lecturing a nn duk abinda nayi ana kae masa info, hka ma layin grandmum dita, shine ranan Abba ya kirani wae daga ynxu ya sake gani na da saurayi ko ma wani iri ne shi to aura Min shi xae yi tunda ba karatu nake son yi ba, Abbana kuma baya magana biyu shiyasa na ji tsoro don ni ban shirya aure ba, ina abun aure a jikina ynxu ni kam, ynxu dae ko xa mu hadu da Uthman a eatry Muke haduwa don ko layin mu ya daina xuwa, shiyasa nayi ma gayen nn abinda nayi masa, amma da don haduwa ya hadu kuma courage dinsa ya burgeni ssae," duk suka kwashe da dariya, Ashnaah tace "eh mana ni dae ina son in yi karatu ssae daga fara remedial kawae sae a aurar dani ko Jami'an ma ban Shiga ba," karfe shidda Khaleel yyi horn gidan small mum dinsa mai gadi ya bude gate ya shiga yyi parkin snn ya juya yana kallon Zeenah da tayi jigum yace "mu shiga" ba musu ta bude mota ta fita shima ya fito ya kulle motar yace "to ae sae ki cire nikaf din" ba musu ta cire, da ganinta kasan a tsorace take, tana biye da shi a baya suka shiga gidan, bbu kowa falon sae Tv dake aiki, ya nuna mata kujera ta xauna snn ya haura sama, tare suka sauko da mum, ta karaso cikin falon tana amsa gaisuwar Zeenah, Meenah ce ta sakko Mum tace Ku tafi sama da ita Amina, Meenah tace "to mu tafi," Zeenah ta mike suka nufi sama tare, har sun fara hawa stairs mum tace Amina ba ki ga Khaleel bne?" Meenah ta juyo tace "au Ashe shine, ina yini ya Khaleel?" Khaleel ya dake yace "qlau" snn suka wuce sama. Yau ma kmr jiya Khaleel ya iso anguwarsu Ashnaah yyi parking yana bin anguwar da kallo a xuciyarsa yana addu'ar Allaah yasa kar yyi wahalar bnxa kmr ta jiya. ~Dr Khaleel~ 12 By Khaleesat Haiydar Khaleel yyi murmushi hangota da yyi tana Tahowa daga layin da ke ranan lahadi ne layin shiru bbu mutane, mayafi ne yafe jikinta yau, ya kafa mata ido har ta karaso titi ta tsaya daga gefen motarsa ta tsayar da abun hawa ta hau, tada motarsa yyi ya hau kan titin ya bi bayan napep din da ta hau. Bae wani sha wahalan bin napep din ba don bbu motoci ssae kan titin, Tafiyar minti kusan goma suka yi keken ya sha kwanan wani layi shima ya bi bayansa, dai dai gate din wani duplex mai napep din ya paka, Khaleel yyi parkin dan nesa da gidan, Ashnaah ta fito ta mika masa kudinsa ta shige gida abunta. Khaleel ya fito yana kallon mai gadin dake xaune bakin gate ya karasa ya gaishesa snn yace "wnn yarinyar da ta shiga nan ne gidansu" mai gadin yace "eh nan ne" Khaleel yace "ok, mai gidan na ciki ne?" Mai gadin yyi shiru snn yace "da matsala ne" Khaleel ya girgixa kansa yace "ko daya, kawae na xata sa ni a kwana tayi da tace nn ne gidansu, ynxu dae ka min sallama da mai gidan in yana ciki" Mai gadin ya mike ya shiga ciki, Khaleel ya xauna yana murmushi, ba a dau lkci ba mai gadin ya dawo ya masa iso har balcony ya nuna masa kujera ya xauna snn ya koma bakin aikinsa, bude kofar falon aka yi wani mutumi da baxae wuce shekaru hamsin ba ya fito yana kallon Khaleel ya basa hannu Khaleel ya ki amsa ya sunkuyar da kansa snn ya gaishesa da ladabi, Mahaifin Ashnaah ya xauna snn ya shiga tambayarsa daga ina, Khaleel yyi shiru yana kkrin tuna sunan da ya gani jikin receipt din Ashnaah snn da sauri ya maxa yace "dama tare da Fateemah muke shine tace in shigo in gaida ka," shiru Abban Ashnaah yyi, sae kuma ya dan yi murmushi yace "to nagode" Khaleel yace "to ni xan koma Abba" Abba ya kuma masa godiya snn ya mike ya bar balconyn Abba ya wuce ciki. Dakin mum din Ashnaah ya nufa ran sa a bace, Ashnaah na kwance tana danna waya, mum dinta kuma na kallon wani program ita da Ashraf, ya tura kofan duk suka juya da sauri, Abba na nuna Ashnaah yace "lallai kin rika Fateema, har ni xa ki turo ma wani ya xo ya gaida ni ko, wato ni kika raina, to daga yau na yanke xuwan ki makaranta a gidan nn, in fact ko nn da gate bana son ki sake fita, wayar Hannun ki kuma Ki kai min shi Daki ynxun nn" yana kai wa nn ya fice daga Dakin, kuka Ashnaah ta fashe da tana kallon mum dinta dake kallonta da mmki, "Ashnaah wa kika tura ma Abbanki" cikin kuka ssae tace "wllh ban sani ba mum," Mum dinta tace "to daga ina kike ynxu" tace "daga gidan inna wllh nake mum, ni ban turo kowa ba" ta karashe maganar tana kuka ssae, mikewa Mum tayi ta fice daga Dakin, sae kuka Ashnaah take, usman ta kira bugu biyu ya daga a fusace ta fara magana "kai ne ka xo gidanmu yau?" Ya dan yi shiru snn yace "ni kuma?, kin manta ina Abuja?" Kashe wayar tayi ta kuma saka kuka don cikin samarinta Usman kadae ne yasan gidansu, kashe wayar tayi gaba daya don ma kar ya kuma kiranta, mum ta dawo ranta a bace tace "ki bar dauko min mgna Ashnaah, mahaifin ki gani yake kmr ni ke xuga ki ni fa ba ruwana ynxu gashi ni ma kin ja min, in kuma auren kike so to ae shkkn." Kuka kawae Ashnaah take duk jikinta yyi sanyi, to waye wnn yyi mata hka, gashi Abba ya dakatar da ita daga xuwa makaranta. Har Khaleel ya isa gida murmushin dake dauke a fuskarsa tun bayan fitansa gidansu Ashnaah Bae bace ba, falonsu ya shiga ya tarda Abbansa xaune a falo da wani abokinsa, ya karasa cikin falon ya gaishesu, Abokin Abban nasa yace "har yau dae ka ki aure ko Khaleel ga Ma'aruf ynxu 'ya yansa har uku, Khaleel yyi murmushi yana shafa kansa yace " ni ma na kusa Abba, in Allah ya yrda watan da xa mu shiga" Abbansa ya sace kallonsa , Khaleel yyi dariya yace "Allah kuwa Abba na samu mata ynxu" Abban nasa yace "to Allah yasa" mikewa yyi ya masu sallama xae haura sama announcement din da ya ji ana yi a Tv yasa ya juya da sauri yana kallon tvn, murmushi yyi ganin hoton Zeenah boldly kan screen din Tvn snn ya haura sama. Satin Ashnaah biyu a gida bata je makaranta ba duk ta fice hayyacinta ta xama abun tausayi ga shi Abba ya amshe mata waya, duk irin lallaba Abba da mum dinta ta dinga yi tana basa hkuri hkn vae sanya ya canxa hkuncin da ya yanke ma Ashnaah ba don Bae yrda bata san daga inda mutumin yake ba, wani amininsa mum ta kira tayi ma bayanin komai don har inna ma yaki saurarenta, ranan da safe aminin nasa ya xo, bayan sun gaisa aminin yasa a kira masa Ashnaah, ta shigo falon da hijab dinta har kasa ta durkusa ta gaida abokin Baban nata, shi dae Abbanta Bae ko kalleta ba, Alhaji Salisu yace "Ashnaah me yasa Baki jin maganan iyayen ki ne?" Kasa cewa komai tayi kanta a Kasa, fada ya shiga yi mata daga karshe yace bbu ruwanta da ko wani saurayi daga ynxu har sae ta gama karatu, tace "to Abba ngdd" Abbanta yace " Allah yasa ya shiga kunnenta, so nawa Mike yin hkn da ita, Alhaju Salisu yace wnn kuma tsakanina da ita na Alhaji, tashi ji tafi gobe ki shirya ki tafi makaranta, Ashnaah taji ddi ssae, kuma tayi vow a xuciyarta daga ynxu bata sake kula saurayi, har usman ma ta bar kulasa don bbu abinda take so kmr karatu a rayuwarta. Karfe biyar na yamma Khaleel ya shigo falonsu Meenah, mai aiki kadae ce a falon tana shara, ya xauna bayan ya amsa gaisuwarta yace "masu gidan basa nn ne" tace "Anty Amina da bakuwa ce kadae a gidan, Momy ta fita, sama ya nufa ya bude kofar Dakin Meenah, Zeenah ce xaune gaban madubi tana comb din gashinta da ya kusa bayanta, ta juya da sauri sae kuma ta mike ganin Khaleel ne ta dauki hijab dinta ta rufe kanta tace "ina yini ya Khaleel" yyi murmushi ya amsa yana kallon ta, Meenah ce ta fito daga bayi tace "haba meye hka Ya Khaleel xaka shigo ma mutane Daki ba sallama in mutum bbu kaya jikinsa fa" Khaleel yyi shiru yana kallonta, hararansa tayi ta koma bayi da sauri ta sa key don tasan me xae biyo baya, yyi murmushi a xuciyarsa yace"Allah ya taimake ki yarinya" waya ya Ciro a aljihunsa ya mika ma Zeenah yace "gashi xa mu dinga magana, hope ba matsala dae" ta gyada masa kai ta karbi wayan snn yyi mata sallama ya wuce. Ashnaah ta karasa gun da motar usman yake da sauri a dan tsorace tace don Allah ka dinga rufa min asiri ya usman,ba na maka bayanin komae ba wae, ynxu idan wani ya ganmu ya je ya gaya ma Abbana fa" da dan damuwa usman yace "to ya kike son in yi Ashnaah yau fa sati uku Rabon da in ganki ga shi ke ba waya ba, to a ina xan ganki in ba nn ba" Ashnaah na kalle kalle kmr munafuka tace ka ga mu hadu a eatryn da ka taba kai ni ranan" yace to da yaushe?" Tace "karfe hudu xan bar makaranta sae mu hadu a can kawae, ki ban xo ba ka jirani" yace to ynxu me kike da baxa mu tafi ba, tace tutorial Muke, tana kai wa nn tayi gaba da sauri, shi ko yyi reverse ya bar wajen. ~Dr Khaleel~ 13 By Khaleesat Haiydar Karfe hudu saura Ashnaah ta bar sch bayan tayi la'asar a mosque, a dai daita sahu ta d auka ta nufi Eatryn da tace Usman ya jirata, bata yi mmkin ganinsa xaune yana jiranta ba, ta ja kujera ta xauna kujeran dake kallon nasa, shi kam sae bin ta da kallo yake, ta dan yi tagumi tana kallon sa, ya sauke ajiyar xuciya yace "me xa a kawo maki," ta girgixa kai tace "aa ni a koshe nake kuma ban ma dde da shan soft drink ba a makaranta" Bae ce komae ba sae kallonta da yake, hkn yasa tace "ya usman ba laifina bne wllh, Abba baya son ganina da kowa ne, aurar da ni yace xae yi idan ya kuma gani na da saurayi," Usman yace "to muyi aurenmu mana Ashnaah, wllh ina sonki tsakanina da Allah, xan bari ki ci gaba da karatun ki har kice kin gaji Ashnaah, yhu won't regret marryin me" Ashnaah tayi masa wani mugun kallo tace "ta baxan yi ba din, yar yarinya da ni xaka wani dinga kira min aure? Am just 17 fa ko ka manta ne xaka dinga ce min aure" kmr xata yi kuka ta karashe maganar. Usman yyi shiru yana kallonta, juyawa tayi da xummar kallon agogon dake manne da bango taga karfe nawa suka yi ido hudu da Abbanta dake xaune da wasu mutane sun kai biyar da gani abu suke tattaunawa, Alhaji Salisu ta gani a gefenta shima yana kallonta, mikewa tayi da sauri kuma a rude ta bar eatry din, usman ya bi ta da kallon mamaki don shi Bae san Abbanta ba, ya mike ya bita da sauri, ko da ya fita har ta hau Napep. A rude Ashnaah ta isa gida ta dinga rusa ma mum dinta kuka, mum dinta duk ta rude tana tambayarta me ya faru hka ma Ashraf, da kyar ta shiga gaya masu abinda ya faru, mum dinta ta mata wani mugun kallo ta fice ta bar mata dakin kawae. Gidan inna ta nufa tana kuka, inna duk ta rude tana tambayar me ya faru, cikin kuka ta yi mata bayani ita ma, inna tace "shine xaki daga hankalin ki uwa kin kashe dan mutum, kai ni fa Adamu ya fara kai ni iyaka, to ya xo nn ya same ki in ya isa in ga, hka kawae duk ya bi ya takura ki don shine ya haife ki" Khaleel ya tsura ma lafiyayyun xannuwan dake kwance cikin akwatin dake gabansa ido snn ya ciro wani blue mai kyau da wani colour daban ya ajiye ma mum dinsa yace "ga wnn ummi" Ummi tace "aa ka bar mata kayanta kawae," yace "ae ni na baki mum" ya cire wasu uku ya dauki daya yace "ke ma mum ga naki" small mum dinsa tace "aa da ka barsu kawae Khaleel" ajiye mata yyi kusa da ita ya rufe akwatin, Ummi tace "su kuma biyun hannunka fa" yace "Ameesha xan ba daya, dayan kuma ina da warce xan ba," mum ce ta komar da lafiyayyun akwatunan har shidda inda suke, shi kuma ya fice daga Dakin, mum tayi dariya tace "kai! Allah yyi, sae dae kuma an ki kawo mana ita mu gani." Washegari lahadi Ashnaah na kwance Dakin grand mum dinta duk ta rasa me ke mata ddi ga shi Abba Bae xo ba har lkcn bare ta ji hukuncin da xae yanke mata , to ko wani hukuncin xae yanke mata wnn karan kuma, wasu hawaye suka shiga gangarowa daga idonta, duk Usman ne ya ja mata komai. Karfe uku na yammacin ranan Abban Ashnaah na xaune falo yana duba jaridar da Bae duba ba da safe mai gadi ya danna kararrawar falon Ashfat ta bude yace da ita ana sallama da Alhaji, ta nufi falo ta ba Abbanta sakon snn ta wuce sama abunta. Mikewa Abba yyi Da yake daga anguwa yake har lkcin manyan kaya ne jikinsa ya fita xuwa gun bakin nasa, mamakin ganin bakin yyi su uku kuma duk Bae san su ba, yyi masu sannu da xuwa snn ya shigar da su har xuwa falonsa aka kuma gaggaisawa, da kansa ya kwaso masu ruwa da lemo a fridge suka masa godiya snn ya koma ya xauna. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 14.... Shiru Abba yyi da mugun mamaki yana kallonsu jin me ke tafe da su, can ganin kar ya maida kansa karamin mutum a gabansu yyi saurin cewa "Eh hka muka yi da ita, amma bn yi tunanin yau xata sa ya turo Ku ba, bari in kira yan uwana ayi komae gaban su kun ga ba dadi inyi komae gaban kai na" suka ce "gskya ne wnn, ba matsala xa mu jira su in Allah ya yrda" Abba ya Mike yana jin jina abinda Ashnaah tayi a ransa, lallai Ashnaah ta fi karfinsa ta nuna masa iyakarsa, wato kan yace mata komae kan inda ya ganta jiya da saurayi bari ta sa a kawo masa gaisuwa, sama ya nufa xuciyarsa na tafarfasa ya shiga dakinsa ya dauki waya ya shiga kiran wasu daga yan uwansa da abokinsa Alhaji Salisu, ba a dau lkci ba duk suka iso gidan, duk suka yi mamakin abinda suka ga Abban Ashnaah na shirin yi kuma ba tare da saninsu ba don Ashnaah yarinya ce karama amma bbu wanda yyi query dinsa ganin bakin, aka yi duk abinda ya kamata bakin suka bada dubu hamsin kudin gaisuwa, suka kuma kirgo dubu Dari suka bada kudin sadaki, suka kuma bada kudin da xa'a siya wasu abubuwan da ya kamata da basu kawo ba, mai gadi aka sa ya shisshigo da akwatunan da suka kawo na gaisuwa, nan take Abban Ashnaah yasa aka sa ranan daurin aure, wata daya kacal, nan da sati biyu kuma xa'a kawo lefe, kallonsa kawae yan uwansa ke yi da mamaki, sae kusan la'asar bakin suka bar gidan bayan sun rakasu har bakin mota ana ta godiya, ita dae Momy tana ta mamakin meeting din da ake yi a fali ba tare da ya sanar da ita xae yi baki ba, ko falo ba su shiga ba daga rakiyan da suka yi Alhaji Salisu yace "ynxu Adamu duk maganar da na maka jiya Ashe baka dauka ba, abinda kayi a tunanin ka ya dace knn, did yhu think dis is d ryt decision" Abban Ashnaah yyi murmushin takaici ya ma rasa me xae ce ma abokin nasa, nan yan uwansa suka hau sa da fada wae ya nuna masu ba su suka Haifa masa Fateemah ba kuma da sun san kiran da ya musu knn da bbu me xuwa tunda lkcn da yace a kawo gaisuwar Bae nemi shawararsu ba, Abba yace "mu shiga ciki in maku bayanin komai, ko kadan banda laifi a nn, hasalima mutanan nn rana tsaka kawae na gansu" nan Abban Ashnaah yyi masu bayanin abinda ya faru tun daga ran da ya hana Ashnaah kula samari har ixuwa yau a cewarsa da ta nuna masa iyakarsa tasa aka kawo gaisuwa ba tare da ya sani ba, duk kowa yyi shiru da mamaki yana kallonsa, Alhaji Salisu yace "anya Ashnaah xata iya hka Adamu, gani nake fa kmr set up ne wnn ni dae, ynxu dae tana ina?" Abba yace "set up fa kace, to ni tun jiya da na dawo gidan nn ban ganta ba tana gidan inna, ae bbu abinda xae sa ni janye ra'ayina na aurar da yarinyar nn nan da wata daya, ba dae aure take so ba, xan aurar da ita" su kam yan uwan Abba Kasa cewa komae suka yi don abun ya daure masu kai. Abba na raka yan uwansa ya dauki wayarsa ya kira Momy tana dagawa yace ta sakko yana jiranta a Kasa, ba a dau lkci ba ta sakko ta shigo falon, ta dinga bin akwatuna da kudin da ta gani da kallon mamaki tace "wnn kuma fa Alhaji" da kyar ta iya masa tambayar don tuni jikinta yyi sanyi, bbu yabo bbu fallasa yace "Ah! yar ki ta turo a kawo min gaisuwa da kudin sadakinta" Momy tace "ya ta kuma?" A tsorace tayi masa tambayar, yyi bnxa da ita ya haura sama abunsa, kuka Momy ta saka tana tunanin anya Ashnaah ce xata yi hka kuwa?. Khaleel ya fada kan gado ya fashe da wata dariya yana shafa kansa snn ya mike xaune da sauri yace "yes! It all worked well at last". Da kyar Ashnaah ta bude kofar falonsu tana lekan falon, har lkcin jikinta Bae daina rawan da yake ba tun lkcn da kiran Abba ya shigo wayar inna wae yana kiranta hankalinta ya Kasa kwanciya, ta juya tana kallon inna da ke bayanta, inna tace " mu je mana kin tsaya kmr warce ta ga mugun abu, mu je in ji kiran da yake maki" Ashnaah ta shiga falon inna na biye da ita a baya. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 15..... Khaleel ne xaune office dinsa aka kwankwasa masa kofa ya bada ixini aka shigo wato nurse ta shigo ta gaishesa snn tace "Dr ne yace in kira ka can sama" Khaleel ya gyada mata kai ta juya ta fita snn ya mike ya fita daga office din ya nufi office din dad din Ameesha, yana tsaye Khaleel ya samesa a office din, Khaleel ya xauna snn ya gaishesa, ya juya yana kallon Khaleel snn ya ja kujera ya xauna ya fara magana a nutse "Khaleel don't tel me that duk son da Ameesha ke maka ynxu baka sani ba," Khaleel yyi shiru yana kallonsa, ya suke ajiyar xuciya snn ya ci gaba kmr hka "wacce yarinya kke shirin aure ynxu?" Khaleel ya kauda kansa yace "budurwa ta ce mun dde tare" Abban Ameesha ya dan yi shiru snn yace "shknn tashi ka tafi" mikewa Khaleel yyi ya fice daga office din nn da nn ransa ya bace ae ko me xae faru bbu abinda xae sa shi auren Ameesha. Ashnaah na kwance dakinta da daddare bayan inna ta koma gidan ta duk abun duniya ya isheta tun safe bbu wanda ya sake mata a gidan gashi har inna ta tafi Abba ya ki fadin kiran me yake mata, Ashfa ce ta shigo Dakin ta ce mata Abba na kiranta, Ashnaah ta mike da kyar gabanta na faduwa ta sauka kasa xuwa gun abban, Momy ma na xaune falon ta dan rabe jikin kujera tace "ga ni Abba" wasu kudade ta ga ya jefa mata yace "ga kudin gaisuwan da sadakin da kika sa aka kawo ma ni, amma ki sani ko kwandala ta baxae yi ciwon kai ba wnn auren naki, kuma kar ki taba nuna Kinsan ni ki je can ki nemi wani uban, xan maki alfarma daya in daura maki aure amma bayan nn ko hanyar gida na kar ki nuna kin sani, snn bbu me min biki a gidana a je can gidan mijin naki ayi" Tunda ya fara magana Ashnaah ke kallonsa kmr wata wawiya, ko kadan bata fahimce me yake cewa ba, anya ma da ita yake kuwa, juyawa tayi ta ga bbu kowa bayanta ta kuma kallonsa da sauri tace "Abba ban gane ba," tsawa Abba ya daka mata yace "get out dama bana bukatar ganewarki" mikewa tayi da sauri tana kallon Momynta taga kuka take, sae ita ma ta fashe da kukan tace "don Allah ban gane ba Abba" mikewa da Abbanta yyi yasa ta bar wajen da sauri ta haura sama tana kuka. Ba karamin tashin hankali Ashnaah ta shiga ba bayan Ashfa ta mata bayanin abinda ya faru, ta mike da gudu ta nufi dakin momynta ta dinga rusa mata kuka wae ita wllh bata turo kowa ba bata san ko waye bane Sharri yake mata, Momy taki ko da kallon inda take, hkn yasa ta fice daga dakin ta koma dakinta ta dauki hijab dinta ta sauka kasa da sauri xata gidan inna amma mai gadi yace abbanta yace kar ya bari ta fita, Ashnaah ta rasa me ke mata ddi a duniya sae rusa kuka take ta daura hannu a ka, to waye wnn ke Neman ruin din mata rayuwarta, a ina ta san shi, tasan usman baxae mata hka ba, Allah ma yasa shi ne abun xae fi xuwa mata da sauki, da kyar ta koma balcony ta xube kasa nan tana ci gaba da Kukanta, tana nan har kusan rana mai gadi ya shigo balcony rike da envelop a hannunsa xae danna bell ta mike da sauri ta fixge a hannunsa snn ta shiga duba menene a ciki, IV ta gani gabanta yyi mugun faduwa ta bude da sauri, kan sunanta idonta ya fara sauka snn Khaleel Muh'd, mutuwar tsaye tayi a gurin xuciyarta na ci gaba da nanata sunan Khaleel, tayi wurgi da envelop din hannunta ta fasa wani ihu tayi cikin gida da gudu ta shige dakin mum dinta tana kuka tana cewa "wllh Momy ban sansa ba, ban taba jin sunansa ba, kin ga wae Khaleel, ni tunda aka haifeni ma ban taba jin sunan ba, don Allah Ku ceci rayuwata kar Ku hada ni da shi momy kila ma kudi yake so yyi da ni wllh" kallonta kawae Momy ta tsaya yi ita ma jikinta yyi sanyi, to waye wnn ya xo Neman auren 'yar ta, tasan ko da wasa ynxu baxata tunkari mai gidan ta da wnn mgnan ba. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 16..... Ummi tayi shiru tana kallon Khaleel snn tace "to don me baxa su yi taron biki ba Khaleel" Khaleel ya daga kafada yace "basa taron biki wae su," Mikewa yyi yace bari in je inyi wanka ummi, Ummi tace "to ynxu har biki ya karato baxa ka kawo min yarinyar ba inga" Ya koma ya xauna yace "kar ki damu ummina har sae kin gaji da ganinta, bana son tana fita ne ynxu, kwana nawa ne ya rage ki kwantar da hankalin ki" Tace "to Allah sa ayi a sa'a yasa tsohuwar gida ce" ficewa Khaleel yyi Bae ce komai ba. Ana ta shirye shirye gidansu Ashnaah don yau kwana biyar ya rage a daura mata aure, mamaki kawae take wae ita xa ayi ma aure, wae yaushe tayi birthday dinta na shekara sha bakwae ne ma dae, ko wata biyu ba ayi ba, shine wae xa a mata aure da wanda ma bata taba jin sunansa ba a cewarta, tunanin hkn nasa ta kukan takaici, Abba kam ca yyi bashi da ko sisin yi mata kayan daki Bae yi wnn budget din ba na wnn watan, takaici yyi ma Momy yawa ta rasa ynda xata yi, har da xata hadasa da mahaifiyarsa sae gashi amininsa da yayansa sun mata iya ynda xa su iya, da ka ga inna kasan tana cikin farin ciki, ita dae ayi a daura aure a fitar da jikarta waje, ko kadan bata ko maganan mijin da aka ba jikar ta ta. Ranar Juma'ah bayan an sauko daga masallaci aka daura auren Khaleel da Ashnaah, daurin auren da ya samu hallatar jama'a da dama, Khaleel ya nufi motarsa yana murmushin da shi kadae yasan dalilinsa bayan ya gama gaisawa da mutane da dama dake masa Allah sanya alkhairi da fatan xaman lfya da amaryarsa, frnds dinsa suka bi sa suna kiransa da ango cikin xolaya, ya hade rae yace "irin wnn wasan ne kuma ban so, Ku bari ran da na xama angon kwa kirani da hkn" ba su bar tsokanansa ba har suka bar wajen da motarsu, Najeeb yace "bari mu je mu dauko amaryarmu tunda ba biki." Ashnaah ta mike tsaye da kyar ta dauki lafiyayyan lace din da kanwar mum dinta ta fito mata da ta sa, kkrin mayar da hawayen idonta take, taki barin Antyn ta dake ta lallashinta tun jiya ta gani don ta mata alkawarin daina koke koken da take, bbu abinda ta sa a cikinta ranan sae dan tean da aka tilastata ta sha, ba a wani yi mata make up ba ranan gaba daya, kawayenta na makaranta duk suka ji tausayinta, kowannensu na tunanin in shi ne aka ma hka ya xae yi. Karfe shidda saura Ashnaah ta sauka kasa da mayafi lullube fuskarta xuwa falon Abbanta kmr ynda aka umarceta, kallo daya ya mata ya dauke kansa, ta karaso a sanyaye ta durkusa gabansa ta shiga xubda a hawaye cikin rawan murya tace "don Allah don annabi Abba kayi hkuri ka yafe min," kasa ci gaba tayi ta shiga rusa masa kuka ta kife kanta kan kujerar da yake xaune, ya cire glass din idonsa yace "tashi ki je Allah yyi maki albarka ya Baku xaman lafiya ke da mijin ki" Kasa dago kanta tayi hawaye na ci gaba da xuba idonta a raunane tace "to Abba karatuna fa" da kmr baxae ce komae ba sae kuma yace "da kina son karatun kika xabi aure" ta dago kanta da sauri cikin kuka tace "wllh Abba sharri aka min ni bance kowa ya turo ba, ka yrda da ni" Abba na kallonta yace "sharri aka maki?" Ta gyada masa kai tace "eh Abba ni ban turo maka kowa ba wllh" [10/10, 6:36 AM] ‪+234 701 117 6189‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 17..... Abba ya tsura mata ido snn yace "to wa ya turo sa" Ashnaah ta shiga share hawayen fuskarta tana girgixa masa kai tace "wllh Abba ban san wanda ya turo sa ba, ni ban san shi ba, ban san daga ina yake ba," tsawa Abba ya daka mata a fusace yace "ni kike ce ma baki san sa ba" Ashnaah ta fashe da wani sabon kukan tace "Allah Abba ban san shi ba sharri yake min, Abba ya kuma daka mata tsawan yace " tashi ki ban waje" kin tashi tayi ta ci gaba da rusa masa kuka tana cewa ya yrda da ita, mikewa Abba yyi a fusace hkn yasa ta tashi da sauri ta bar wajen ta nufi sama, kasa komawa ya xauna yyi ya shiga kai koma a falon yana naxarin abinda Ashnaah ke cewa ynxu, wayarsa ya dauka ya kira mum dinta yace ta same shi falonsa, ba a dau lkci ba ta sakko kasa, ya nemi kujera ya xauna yana kallonta yace "A ina Ashnaah suka hadu da wnn yaro da ke shirin aurenta?" Momy tace "sae yau kasan da wnn tambayar?' Tun da baka yi ta ba sae da aka daura aure, to ko kadan Ashnaah bata san daga inda mutumin yake ba, to da yake na ga Neman Kai kke da 'yar taka shi yasa ban katse maku hanxarin Ku na aurar da ita ba," Abba ya Mike tsaye ransa a bace yace "kar Ku raina min hankali, ni xa Ku maida yaro ko karamin mutum, Ku hada baki ke da yar ki Ku xo nn Ku caxa min kai, to bari kiji ko da ma da gsken ne bata san mutumin nn ba wllh wllh bbu abinda xae hanata xaman aure da shi, in an kai ta gidan nasa ma ya yanka ta karewar komae knn, yarinyar da bata dauki maganar uban da ya haifeta a bakin komae ba meye amfaninta, ba abun kunya bane ba ma ace kmr ni ana ganin 'ya ta gidan cin abinci da holewa da saurayi, da na hanata wnn sae ta koma wancan sbda ta raina ni ke kuma kina kare ta, to ki koma Ki gaya mata plan din naku Bae yi aiki ba," ya ja tsaki ya ce "mutanan bnxa kawae" dakinsa ya nufa ransa a bace, kan ya shiga ya juya yana kallon Momy da hawaye ya gama wanke mata fuska yace "kar kuma yar nn ta kuskura ta kwana gidana yau, maxa ana magariba a tafi da ita dakin mijinta" yana kai wa nn ya shige dakinsa. Momy ta nufi sama jikinta a sanyaye tana ci gaba da hawayen da take. Dai dai lkcn wa enda suka je yi ma Ashnaah Jere suka dawo kowa na yaba gidan da xa a kaita, kanwar momy ta ja ta xuwa daki tace "haba yaya kukan meye wnn baxa ki daina ba tun daxu, wllh Ki kwantar da hankalin ki, ni na tabbatar maki wnn mutumin ba don ya cutar da ita yyi hka ba, kawae tsabar sonta ne, sae kin ga gidan wllh, Ashnaah ta samu gidan Hutu ni na tabbatar maki yaya," Momy tace "to da kike wnn maganan kin san aikin da mutumin yake ne" Anty farida tace "wllh likita ne, kuma ma babban likita snn mahaifinsa ma babban dan kasuwa ne, sae ma kinga ynda yan uwansa suka tarbe mu daxu wllh don duk suna gidan, ki kwantar da hankalin ki kawae yaya, ba mutanan bnxa bne" Momy ta share fuskarta tace "to Allah yasa, shi kuma Adam Allah ya shiryesa ya dawo da shi hanya". Karfe bakwae da kusan rabi aka tafi da Ashnaah gidan mijinta da bata sani, bbu abinda take masu sae aikin kuka a motar, ita takaicin ta bbu wanda ke son yrda da ita idan tace bata san mijin ba, tafiyar kusan minti talatin suka yi kafin suka iso gidan mai gadi ya bude masu gate driven ya ja motar ya shiga ciki ya samu gu yyi parkin, ana bude ma Ashnaah kofa ta fito ta cire mayafin kanta da sauri tana kare ma kantamemen gidan kallo tana huci ae kam mai gidan nn ya aurar ma kansa fitina da tashin hnkli, aka ce ta fito da kafarta na dama bata ko sauraresu ba ta fito da ta hagu abunta kuma da gangan, suka kama yi mata masifa wae bata jin mgna, bata ko kallesu ba ta shiga bin kanwar mum dinta suna biye da su a baya har suka iso babban falon gidan, bbu abinda bbu cikin falon ba jin ddin rayuwa, Antynta ta juya da sauri ganin yan uwan khaleel a falon tace " ke baki da kunya ko Ashnaah, baxa ki rufe fuskar ba, " Ashnaah ta wara idonta da mamaki tace "ji Anty fa, akwae me bina bashi a nan ne ya fadi in ji da har xan rufe masa fuska" ganin ynda antynta ke kallonta jikinta yyi sanyi don ba Karamin nasiha aka mata ba kan su bar gida daxu yasa Ashnaah ta daura mayafin hannunta a kanta fuskarta a daure ta rike kugu tana kare ma mutanan dake xaune falon kallo. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 18..... Mum din Meenah ce ta taso tana kallon Ashnaah duk da jikinta yyi sanyi tace "sannun Ku da xuwa amarya" Ashnaah ta dan yi tsaki ta saki mayafin kanta ta rufe fuskarta da shi, mum din Meenah ta kama hannunta suka nufi sama su anty na biye da su a baya su ma a sanyaye, duk nasihan da aka taru ana ma Ashnaah a Daki kawae shiga kunnenta na Dama yake yana fita ta hagu, duk ta kagu su rabu da ita sae wani kallon banxa take ma Zeenah da Meenah dake dakin su ma suna kallonta, Anty da sauren yan uwan mum duk jikinsu yyi sanyi ssae, ynda kasan ba amarya suka kawo gidan ba ta wani sauke mayafin kanta xuwa kafada tana bin kowa dake dakin da kallo, Meenah da taji kmr ta sake dariyan dake cin ta ta mike kawae ta fice daga dakin Zeenah ta bi bayanta, sae da suka sakko kasa snn Zeenah tace "wnn ita ce amaryar ya Khaleel din wae Meenah" Meenah ta fashe da dariya har da kyakyatawa tace "to gashi kin gane ma idon ki kuwa, dai dai shi ya dauko ma kansa," Zeenah ta kasa cewa komae tana mamakin duk ajin Khaleel ya rasa warce xae auro sae yarinya karama kuma fitsararriya, Meenah tace "ni dae tace xata kawo min iskanci naka da mata duka xan yi wllh, wnn ta wuce kanwata ta uku ma". Sae kusan karfe tara duk aka watse aka bar Ashnaah daga ita sae halinta a gidan, nn fa hankalin ta ya tashi ssae ta soma rera kukan da bata yi ba tunda aka kawota gidan, kasa xaune tayi ta mike tsaye ta shiga xarya a dakin tana rusa kuka tana tunanin to yau wani irin mutumi xa su kwana gida daya da, wa ya sani ma ko dan yankan Kai ne, kila yau ma shine rananta na karshe a duniya, tunanin hkn yasa jikinta ya soma rawa ta fara tunanin to ko dae ta gudu ne kawae, tana cikin yanke decision din taji an bude gate din gidan, xuciyarta ya kusa shige wa cikinta son tsoro, wani sabon kukan ta saki ta durkushe wajen ta daura hannunta a ka tana kiran momynta, can kuma ta mike da sauri jikinta na rawa ta nufi window ta ga irinsa kan ya shigo gidan, har ya gama parkin motarsa a parkin space ya nufo kofar shiga gidan, bata ganin komae sae tall figure dinsa don bbu haske tsakar gidan sae daga can bakin gate, wani sabon kukan ta rushe da ta koma gefen gadonta da sauri ta xauna jikinta na rawa. Takun sa da taji a stairs yasa ta gane har ya shigo gidan ta mike a hnkli ta nufi gun inda ta ga switch din wutan dakin cikin sanda ta kashe wutan dakin snn ta koma da sauri ta xauna xuciyarta na bugawa tayi saurin share hawayen fuskarta da Mayafin jikinta, suma ne kawae bata yi ba da taji ya bude kofa Ashe wani kofa daban ya bude, ta sauke ajiyar xuciya, ta xamo kasan tiles a hnkli ta xauna don ji tayi xaman gadon ma ya gagareta, yau tata ta sameta, ko minti biyar bata yi da sauka kasan tiles din ba baccin tsoro ya sace ta nn xaune, a firgice ta farka jin an bude kofar dakin da take, ta ga mutum tsaye bakin kofa kuma har lkcn wutan Dakin a kashe yake, a hnkli ta mike ta koma kan gadon ta xauna xuciyarta na wani mugun bugu da Bae taba yi ba, shi ko har lkcn yana tsaye bakin kofar, sae a snn tayi da ta sanin kashe wutan dakin ko ba komae ae da ta ga fuskarsa ynxu, shknn har ya kashe ta baxata ga fuskarsa ba knn, ji tayi kmr ta sake fitsari ganin da tayi ya rufe kofar dakin, to ko dae ta fara rokonsa ne kawae ya ceci rayuwarta, ko kuma ta saki ihu kawae, duk da ba wuta dakin amma ana iya ganin inda take, karasowa taga yana yi xuwa gun da take, ta mike da sauri ta isa jikin bango jikinta na bari, nan da nan dubara ya xo mata cikin rawan murya tace "wllh xan caka maka abinda ke hannuna in ka karaso inda nake," tsayawa ta ga yyi cak nn inda yake, ganin hkan yasa ta samu kwarin gwiwa ta ci gaba muryarta a dake tace "in kuma karya ne ka karaso ka ga" komawa taga yyi ya nufi gun switch din dakin nn da nn hankalinta ya tashi ta sake kuka ba tare da ta sani ba ta bi bayansa da sauri muryarta na rawa tace "wllh kar ka kunna min wuta, kana kunna wa xaka sha mamaki," da sauri ya isa gun switch din ganin tana bayansa, kan ya Kai hannunsa ta wani fixgosa da karfi ya fado kanta duk suka fada kasan dakin, ba ita ba shi kansa sae da ya tsorata, ya tura ta daga jikinsa ta kuma rikosa da sauri cikin kuka tace "wllh na ce kar ka kunna min wuta xan baka mamaki," kkrin mikewa tsaye ta fara yi ya fixgota ya kai ta kasa, snn shi ya mike ya nufi gun switch din ya kunna da sauri, xae juya suka kuma cin karo don Magyar har ta taso, ta cukumosa ta rufe fuskarta a kirjinsa tana rusa kuka tana cewa "wllh ka mai da ni gidanmu" ita ko kadan bata ma son ganin fuskarsa, duk da irin kamshin da yake ya dan kwantar mata da hankali, tura ta yyi da karfi ya jinginata da bango ynda xata gansa da kyau, amma kememe taki bude idonta. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 19..... Tsayawa Khaleel yyi yana kallonta har lkcn taki bude idonta, sae wani shishshige wa kirjinsa take tana cewa ya fita ya bar mata dakinta, sae a nn ya ga ashe ma yarinya ce karama, dago kanta yyi yana kallon fuskarta ya watsa mata wani lafiyayyan mari ta bude idonta a gigice ta daura kan fuskarsa, yana murmushin mugun ta yace "kin gane ni" kallonsa ta tsaya yi a tsorace tana kkrin tunano inda ta taba ganin fuskarsa, bata ankara ba ya kuma kai mata wani marin da yafi na da gigitata, ta saka kuka ya shaketa yana mata mugun kallo yace "nace kin gane ni" sae a snn ta tuno inda ta taba ganin sa, da sauri ta shiga gyada masa kai a tsorace, ya sake ta yana mata wani irin kallo yace "sae kin gwammace mutuwar ki da xaman aure a gidana, sae kin yi da kin sanin xuwan ki duniya yarinya, in yhur next lyf, yhu wil Neva raise ur filthy hand to slap a guy" yana kai wa nn yyi murmushin mugun ta yana shafa sajensa ya juya ya nufi kofa, kuka ta saki a rude tace "amma Allah ya isa tsakanina da kai, mugu axxalumi macuci, kai ma sae ka gwammace mutuwar ka da auro ni da kayi ka kawo ni rubabben gidan ka, sae na xame maka jaraba da tashin hnkli" da mamaki ya tsaya kallonta, ta fasa ihu ta durkushe inda take jikinta na raaa ganin ya yo kanta, yyi wani irin ball da ita da karfi har sae da ta buge kanta da gado, snn ya cakumota yana huci, a tsorace ba tare da ta sani ba ta shiga cewa "don Allah kayi hkuri ba da Kai nake ba wllh" janta ya shiga yi ya bude wani kofa dake dakin ya jefata ciki ya fito ya rufe kofar da key, waige waige ta shiga yi a tsorace don muguwar matsoraciya ce ita tana kallon inda ya jefota taga balconyn dakin ne, mikewa tayi ta shiga bubbuga kofar tana rusa kuka amma Bae bude ba, hkn yasa ta dinga xaginsa, bbu irin xagin da bata masa ba amma ba a bude dakin ba, ta sulale Kasa tana cigaba da aikin Kukanta cikin rashin kuxari don duk jikinta ya mutu, a hka bacci ya sace ta, bata san adadin lkcn da ta dauka tana bacci ba taji an bude kofar ta farka a firgice don bata da nauyin bacci, tsaye ta gansa bakin kofa ya fixgota ya jefata cikin dakin snn ya rufe balconyn ya juya ya fice daga Dakin, ta kife kanta kan tiles din dakin ta shiga rera kuka a hankali, can ta dago kai tana kare ma dakinta kallo, ynxu fa shknn wae aure aka mata da wnn xakin da take gani, ba ita ta koma bacci ba sae kusan asuba, bata kuma farka ba sae da gari ya waye, agogo ta kalla baki bude taga bakwae har ya wuce ta mike da sauri ta nufi kofar da take tunanin bathroom ne, alwala ta daura ta fito yin sllh, ta dde xaune kan darduma tana addu'ar Allah yyi mata iyaka da Khaleel daga bisanni ta mike ta shiga bathroom don wanke Bakinta, ido ta xaro ganin ynda idonta ga kumbura tace "tabdi ae baxan bari yyi tunani ya ci nasara a Kai na ba, sae nasa ya raina kansa wllh," ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar20....Cikin hanxari ta gama wanke bakinta ta kuskure da mouth freshner ta tube kayanta ta shiga gun wanka, sabon towel fari ta samu ta dauka ta goge jikinta snn tadaura ta fito ta shiga bubbude wardrobe din dakin don neman inda kayanta suke, undies ta fara ciro wa snn fito da wani lafiyayyen Holland dinta an mata Riga da skirt ta ajiye kan gado ta nufi gaban madubinta ta xauna tana duba man da xata shafa, ta gama shafe shafenta snn ta shiga yi m fuskarta make up lafiyayye, wani hadadden kyau tayi dama ga ta kyakkyawan karshe, ta Mike ta dauki kayanta ta saka, tana cikin daura dankwali gaban madubi aka bude kofar Dakin, duk da ba karamin tsorata tayi ba hkn Bae sa ta daga kai ta kalli wanda ya shigo ba ta wani dake tana kkrin daura dankwalinta, sallamar mace da taji yasa ta juya tana kallon warce xata shigo mata, Rukayya ce kanwarsa ta shigo rike da basket din abincin breakfst, da gani ba sae an gaya mata ba tasan kanwarsa ce don ga kama ta gani, ta wani tsuke baki ta hade rae tanaci gaba da daurin dankwalinta, rukayya ta karaso dakin da dan fara'arta tace "ina kwana Anty amarya?" Ba tare da Ashnaah ta kalleta ba can ciki tace "Qalau" Rukayya ta dan yi jigum inda take tsaye, Ashnaah ko sae faman daurinta take, Rukayya tace"Break fst na kawo" Ashnaah tace "to ae basae kin shigo da shi nn ba mana, ba sae ki barsa can falo ba" Rukayya bata ce komaeba ta juya ta fita jikinta a sanyaye, Ashnaah ta ja dogon tsaki ta shiga fesa turare abunta, Rukayya ta kusan cin karo da yayanta xae haura sama yace "ina xa ki"tace "ca tayi wae in saukar da shi kasa" Khaleel ya bata hanya ta sauka, snn ya haura sama ya nufi Dakin Ashnaah ya buga shi da karfi, har lkcn tana xaune gaban madubi ta gama sa jewelries dinta tana kare ma kwalliyarta kallo, kallo daya tayi masa ta dauke kanta duk da irin faduwar da gabanta yake, ya daka mata wani tsawa yace "a gidanku hka aka koya maki idan kin tashi da safe kar ki fito kiyi aikace aikacen gida" ta juya tana masa wani matsiyacin kallo tace "ae ba yar aiki aka kawo maka ba, sae ka jira ran da....." Wani ihu ta fasa ta mike da sauri ta nufi bayi ganin ya yo kanta, yyi saurin fincikota ya juyo da ita yana kallon fuskarta, ta hadehannayenta biyu jikinta na rawa tace "don Allah kayi hkuri ba da kai nake ba pls" mariya wanka mata ta fasa kuka ya buga bakinta snn ya shiga janta suka fita daga dakin har suka sauko downstairs snn ya jefar da ita tsakiyar makeken falon da ya shigo da ita yace "ki tabbatar every blessed day kin share ko ina na falon nn kin goge snn kin fita waje ma kin share duk compound din nn and dat shud b done every morning as early as possible, motata ma daga dis very moment ke xaki dinga wanke shi duk safiya, snn ki hada breakfast ki kai ma duk masu aikin gidan nn da masu gadi, kowa ki bi sa inda yake ki ajiye masa hka ma lunch da dinner, lastly daga yau ko mai bana son in kara ganin kin shafa a gidan nn bare hoda ko jan baki don ba gidan iyayenki bane nn, ko wa kike tunanin kike ma kwalliya da wnn kodaddiyar fuskar taki" Ashnaah ta mike tsaye tana masa wani matsiyacin kallo tace "Sannu ubana, to wllh bari ka ji, kayi kadan ka kawo ni gidan ka in maka bauta, ashe gidan ka xae rube ba gyara, motar ka kuma xae dafe ba wanki, masu gadin ka dama'aikatan ka kuma xa su mace da yunwa,kwalliya kuma ba sbda wani bnxa nake yi ba don bae isa nayi masa kwalliya ba, shi a su wa" kallonta kawae Khaleel yake da mugun mamaki, da ganin ynda take maganar kasan a tsorace take, ya juya da sauri ya nufi sama Ashnaah ta xaro ido ta bi sa da gudu xuciyarta na mugun bugu. [10/10, 6:37 AM] ‪+234 701 117 6189‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 22.... Zeenat da Meenah ta gani tsaye bakin kofar dakin, duk da bata san sunansu ba ta gane fuskarsu, ta hade rae tana kallon agogon dake manne jikin bangon dakinta ta ga karfe sha biyu saura, Zeenah tace "bacci kike Anty amarya" Ashnaah tayi kmr bata ji ta ba, Meenah ta karaso cikin dakin rike da kulan abinci ta ajiye, Zeenat ma ta shigo ta xauna kan stool din dake gaban madubin dakin tana kallon Ashnaah tace "ya kewa" Ashnaah tace "kewan me" bata jira ne xata ce ba ta mike ta nufi bathroom abunta, Meenah ta kalli Zeenat tace "tashi mu je" mikewa Zeenat tayi a dan sanyaye ta bi bayan Meenah, suna sauka kasa Meenah ta fara mata masifa tana cewa "sae wani shishshige ma yarinya kike tana sha ma mutane kamshi, da gani yar talakawa ce wllh, bnxa da ita kawae xata kawo ma mutane rainin hankali yarinyar da bata wuce kanwar mu ta uku ba, ni ba din momy ba ma bbu abinda xae shigo da ni gidan nn," Zeenat tace "to ae dan sbda ya Khaleel wae, idan batun hka ita ta isa, meye hadina da ita" Meenah na mata wani irin kallo tace "to fa, shi kuma Khaleel din meye hadin ki da shi" Meenah ta fashe da dariya Zeenat dae bata kuma cewa komae ba har suka isa gate dai dai bakin gate suka ci karo da Khaleel yyi parkin motarsa a waje xae shigo, wani mugun kallo yake ma Meenah yace "me ya shigo da ke gidana" bata ko kallesa ba tayi gaba abunta da sauri ta nufi titi, ya kalli Zeenat yace "me kuka xo yi" Zeenat tace "abinci momy ta ba mu mu kawo" yace "ok mu shiga ki dan min abu, xan mayar da ke gida" shiru tayi tana kallonsa, ya juya ya shige gidan, ta juya ta bi sa a hankali. Ashnaah na jin fitarsu Zeenat dama ta mike da sauri ta sauko kasa don ganin me aka kawo mata a kula, jollof ne ya ji nama da plantain, har wani rawa jikinta yake ta bude kulan kasa ta ga lafiyayyen farfesun kaxa, da gudu ta mike ta shige bathroom da sauri ta wanke hannunta ta kuskure baki ta fito ta xauna ta shiga tura abincin ta, Khaleel ya juya yana kallon Zeenat dake tsaye daga bakin kofa yace "abinci xa ki girka min, ko baxa ki iya ba" ta dan yi shiru snn tace "me xa a dafa" ya xauna kan kujera ya dauki remote yana canxa tashar tvn dake aiki yace "simple food, da kika ga ya fi sauri," mikewa yyi yace "mu je in nuna maki kitchen din da kayan abinci" ba musu ta bi bayansa suka isa kitchen din ya Ciro makulli ya bude, ita dae sae kallonsa take da mamaki, to meye na wani rufe kitchen" nuna mata komai yyi ya juya ya fice daga dakin ya nufi sama, Dakin Ashnaah ya bude ta tura kulan gabanta da sauri tana kkrin goge bakinta ta tashi ya shigo dakin, kunya ya kamata gashi da hannu take cin abinci, dariya ya shiga yi yana kallonta, ta wani hade rae har lkcn hannunta na boye bayanta tana masa mugun kallo, yace "duk yunwarce hka" tsaki tayi ta kauda kanta, yana shafa kansa yace "kadan kika fara gani yarinya," juyawa yyi ya fice daga dakin, ta ja tsakin takaici tace "kae dae ne mayunwaci, bnxa kawae" mikewa tayi don takaici ta shige bathroom wanke hannunta, duk sae ta ji abincin ya fice ranta, kamshin soya miya da taji kasa yasa ta kasa xama daki ta sakko kasa, to wa ke girki, bbu kowa falon hkn yasa ta nufi kitchen da sauri, da mamaki take kallon Zeenat, ita dae Zeenah kallo daya tayi mata ta ci gaba da abinda take, Ashnaah tayi tsaki tace "Aikin bnxa, da kawae yyi xaman auren da ke, karewar kawo ki ki masa girki knn" Zeenat ta juya tana kallonta bata dae ce komai va, amma ba karamin bata mata rae kalaman Ashnaah suka yi ba, ita Ashnaah duk tunanin ta kanwarshi ce, ta ja dogon tsaki ta fice daga kitchen din suka kusa cin karo da shi, yana mata mugun kallo yace "me kika sakko yi" hararsa tayi tace "kai me ya sakko da kai xaka min wnn silly tambayar" ya tsaya kallonta daga sama xuwa kasa snn ya wani wanke fuskarta da mari, ta dafe kuncinta a gigice tace ka mareni? " bata rufe baki va ya kuma sauke mata wani, ya fixgota da karfi ya nufi sama da ita ya bude dakinta ya jefata ciki, sae da taga ya kulle kofar snn cikin kuka ta shiga cewa "Allah ya Isar min mugu kawae mahaukaci kuma wllh sae na...." tsit tayi jin ya bude kofar Dakin ta Mike da gudu har tana neman faduwa ta shige bathroom ta kulle kofar da key, ya juya ya fice daga dakin, karfe daya da kusan rabi Zeenat ta gama hada masa Shinkafa da miya ta ajiye masa nn tsakiyar falon, ta dan jingina jikin kujera tana jiran saukowarsa, ta kai minti goma a tsaye sae gashi ya sakko cikin kananan kaya yana kallonta yace "har kin gama" tace "eh gida xan tafi" Bae ce komae ba ya karaso cikin falon ya xauna yana kallon abincin yace "sllh fa" ta dan yi shiru snn tace "idan naje can gida na yi" ya daga kai yana kallonta da kmr baxae ce komae ba sae kuma ya jawo plate ya shiga diban abincin gabansa yace "sae ki ce min kina period" ya daga kai yyi murmushi yana kallonta yace "ki ba hka ba" kasa cewa komae tayi, ya fara cin abincin gabansa yace "ki xo ki diba kema" ta kauda kai tace "na koshi" Bae ce mata komae ba sae cin abincin sa yake, ta kasa daina kallonsa, cokali biyar yyi ya daga kai ya kalleta suka hada ido ta dauke kanta da sauri yyi murmushi ya mike yace "kwashi abincin ki kae min dinnin anjima idan na dawo xan ci, ba musu ta karaso cikin falon ta duka ta kwashe farantin abincin ta nufi dinnin da shi, shi kuma ya haura sama, dakinsa ya shiga ya fara wanke bakinsa a bathroom snn ya fito ya dauki makullin motarsa ya fita, dakin Ashnaah ya nufa, tana xaune kasan dakin ta hade kanta da gwiwa, tana jin an bude kofarta ta dago da sauri, ya hade rae yace "ke nake jira" tayi tsaki ta dauke kanta, ya karaso cikin Dakin ta Mike tsaye a tsorace tace "ni me nayi kuma" ya wani hade rae yace dauki hijab din ki ki fita muje, ta nufi drawer dinta kmr xata yi kuka ta dauki hijab din tasa ya nuna mata kofa ta nufi kofar yana biye da ita a baya, suna sauka downstairs ya kalli Zeenat yace "mu tafi Zeenah" Zeenah ta nufi kofar fita Ashnaah ta juya tana masa kallon bnxa tace "ina xaka kai ni," irin kallon da taga yana mata yasa ta nufi kofa da sauri tana tsaki, Khaleel ya bude seat din gaba yana kallon Zeenat dake tsaye jikin motar yace "shiga" ta dan xaro ido tace "ni" hararanta yyi yace "ki shiga nace" kasa shiga tayi har lkcn tana tsaye, ganin ynda yake kallonta yasa ta dan raba ta gefensa ta shiga gaban motar, Ashnaah dae na kallonsu tayi tsaki ta bude bck seat ta shige abunta a xuciyarta tace "ki ba komae ka xama driverna dae" har suka bar gidan Ashnaah bata kalli gaban motar ba idonta na kan glass kawae, firarsa kawae yake da Zeenat da bata cewa komae, can dae ya juya ya kalleta ya mayar da idonsa kan titi yace "ni kike sharewa ko" ta kallesa tace "ae ina jin ka," Bae kuma ce mata komae ba har suka iso traffic light snn ya juya yana kallonta yace "to me nace na karshe" ko kadan bata san me Khaleel ke cewa ba don duk a takure take a motar sbda Ashnaah dake baya, ta fara kame kame tace "aa ina fa jin ka ya Khaleel" ya kamo hannunta yana kallonta yace "tsoron warcan abar ta bayan mota kike" Zeenat ta fixge hannunta da sauri duk jikinta yyi sanyi, maganar sa tayi confuse dinta, yyi murmushi ya kalli Ashnaah ta madubi yaga murmushi take ma wani mutum dake gefen su cikin lafiyayyen motarsa yana daga mata hannu, Khaleel ya hade rae yana kallonta yace "na ga alamar ke jahila ce da auren nawa a kanki kike ma wani kato dariya" Ashnaah tace "da auren ka a Kansu dae ba ni ba, don har ynxu ni bbu abinda ya raba ni da xama budurwar da nake, ko ina budurwa xata shiga nima xan shiga don ni ba matan auren kowa bace," Khaleel yyi murmushi yana kallonta yace "hka kika ce ko? xaki raina kan ki yarinya, sae kinyi da kin sanin furucin ki" Ashnaah ta tabe baki tace "kai ma hka" Zeenat ta kasa daga kai don tuni suka gama daure mata kai, Khaleel dae yyi murmushi kawae ya ja motarsa, dae dae kofar gidansu Meenah yyi parkin Zeenat ta bude motar xata fita ya riko hannunta yace "bbu sallama" ta sunkuyar da kanta bata ce komae ba, ya dago kanta yana kallon fuskarta, sae kallonsu kawae Ashnaah take da mmki, ba sae an gaya mata ba tasan Zeenat ba kanwarsa bace, nn da nn taji wata mugun tsanarta ya dirar mata a xuciya ta dauke kan ta daga kallonsu da sauri, Khaleel ya saketa yace "ltr da daddare xan xo" Zeenat bata ce komae ba don duk ya birkita mata kwakwalwa, ta fice daga motar da sauri ba tare da ta kuma kallonsa ba, yyi murmushi yyi reverse suka bar anguwar. Khaleel ya gama parkin a parkin space din gidansu ya fito yana kallon Ashnaah yace "ni kike jiran in fiddo ki koh" dauke kanta tayi, tayi kmr bata san da ita yake ba, ya bude back seat ya fixgota ta kusan faduwa ya rufe motarsa ya nufi cikin gida, kin bin sa tayi har yyi nisa ya juya ya ganta tsaye, ya dawo a fusace ta shiga tahowa da sauri dae dae gabanta ya ja burki yana mata mugun kallo yace "Ki dinga kiyayata fa" dauke kai tayi yyi kwafa ya ci gaba da tafiyarsa ta shiga binsa tana masa mugun kallo har suka shigo falonsu, sama ya nufa ita kuma tayi xaman ta kan kujera fuskarta a daure, ko ba a gaya mata ba ta ga alamar kmr gidansu ya kawota, ba a dau lkci ba ya sakko tare da mum dinsa da wasu yan uwanta suka shigo falon, kallo daya Ashnaah tayi masu ta dauke kai, suka xaxxauna suna mata sannu da xuwa taki ko da kallon inda suke, momy ce tayi karfin hali tace "ina yini amarya" Ashnaah ta dan kalleta ta maxa ta dauke kai snn tana wasa da xoben hannunta tace "lfya lau" Khaleel ji yyi kmr an Sara masa guduma a ka, ya kasa daina kallon Ashnaah ga wani kunya da ya ji kmr ya nutse, yan uwan momy suka mike kowa ya nufi sama, momy kam bata fasa cewa ya bakunta ba, ba kunya ba tsoron Allah Ashnaah tace "da gdya" momy ta mike tace "bari a kawo maki ruwan sanyi" Ashnaah tace "to" kuma ko ba a gaya mata va tasan mahaifiyar Khaleel ce don ga kama, kitchen momy ta nufa, Khaleel ya taso da sauri ya isa gabanta yace "ita mum din tawa kika ki gaidawa sbda ba a maki tarbiya gidan Ku ba" Ashnaah tayi tsaki tace "a hka ka gan ni ka aura ae, bnyi niyyar gaidatan ba sae me" ta ja dogon tsaki tana hararansa ta maida hankalinta kan kallon da take, ransa yyi mugun bace ya mike da kyar ya dunkule hannayensa ya haura sama Ashnaah ta bi sa da harara ta tabe baki, momy ta dawo falo rike da farantin Ashnaah ta mike ta dan Risina ta karba tace "dama kin bar shi momy daga gida Muke ae" momy tace "shine kuma baxa a sha ruwa ba don daga gida ake" sae da momy ta xauna snn Ashnaah ta sauko har kasa ta gaisheta, momy tace "lfya lau Fateemah ya kewan gida" Ashnaah ta dan yi murmushi bata ce komae ba, momy ta kira Rukayya ta sakko snn suka wuce sama da Ashnaah, tsaf momy ta kare Ashnaah gaban yan uwanta dake ta mitan ba yar gidan mutunci Khaleel ya auro va, bbu ynda suka iya da Yayar tasu duk suka ja bakin su suka yi shiru, karfe biyar da kusan rabi duk bakin dake gidan tun biki suka watse kowa ya kama gabansa, Khaleel ya kai kanwar mum dinsa da suke daki daya gida, ssae yaji kunyar fadan da take masa wae ya je ya auro yarinyar da va yar gidan mutunci va don bata da kunya surkarta ce xata gaisheta kuma ta amsa, in ma su baxata mutuntasu ba ae ya kamata ta mutunta uwar mijinta, har muka bar gidan ko sallama bata fito tayi mana ba sbda rashin kunya, ta girgixa kai tace "me ya kai ka Khaleel, a ina ka samo ta, kai ynxu kaji ddin abinda tayi ma uwarka, yarinyar da bata wuce xama jikarta ba idan da kae mace ne" Khaleel ya kasa cewa komae xuciyarsa sae tafarfasa yake yana tunanin me xae ma Ashnaah ya ji sanyi, irin fadar da mum din Meenah tayi masa knn jiya da daddare wae yaje ya auro ya Mara mutunci wato fitsara xata dinga yi ma danginsa ko, Khaleel yyi murmushi xuciyarsa na raya masa irin abinda xae ma Ashnaah, har ta gama bambaminta Khaleel Bae ce komae ba, bayan driving din kusan minti talatin ya isa gidanta ya ajiye ta ya bata hkuri ssae snn ya kama hanyar gida xuciyarsa na tafarfasa. 45 mins · Khaleesat Haiydar... [10/10, 6:37 AM] ‪+234 701 117 6189‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 23..... Karfe takwas da kusan rabi Khaleel ya shigo gidansu, bbu kowa falo sae Rukayya da ke dan goge goge, Khaleel yace "Abba ya dawo ne ke" Rukayya tayi masa sannu da xuwa snn tace ae yana Abuja Bae dawo ba, yace "ok ummi fa?" Rukayya tace "tana daki" yace "yarinyar nn fa" rukayya tace "wace yarinya" ya harareta yace "warce na kawo gidan nn" Rukayya tace "oh ita ma tana sama ina jin, ga abinci can ummi ta ajiye maka a dinning" Bae kuma kallonta ba ya nufi sama ya bude Dakin umminsa ya shiga, ya samu ummi na sllh, Ashnaah kuma na xaune kasan carpet daga kusa da gado tana kallo don ita tayi sllhnta, Bae ko kalleta ba ita ma hka, ya nemi kujera ya xauna yana kallon wristwatch din hannunsa Allah Allah kawae yake ummi ta idar su bar gidan da Ashnaah, ummi ta sallame ta gama adduarta tace "ka dawo Khaleel, amma ka jima, ga abincin ka can kan dinnin" yace "ni na ci abinci gidan mum ummi, gida xamu wuce ynxu dare yyi" Ashnaah ta daga kai tana kallonsa tace "amma ca kayi min a nn xamu kwana fa ka manta ne" Ummi tace "nima dae hka tace min, kuma kace xa ku tafi ynxu ga shi dare yyi" kasa cewa komae Khaleel yyi sae kallon Ashnaah yake, ta hararesa ta ci gaba da kallonta, ya mike ba don ransa ya so ba ko kadan sae don Bae iya jayayya da umminsa yace "to shkkn ummi bari in yi wanka," yana fita ummi ta juya tana kallon Ashnaah tace "to tashi ki kai masa abincin da na ajiye masa kan dinnin Fateemah, sae ki ce rukayya ta nuna maki dakin sa" Ran Ashnaah Bae so ba amma bata mata musu ba ta mike tace "to momy" snn ta fita kasa xuwa falo, sae da ta dauko farantin abincin snn tana kallon rukayya bbu yabo bbu fallasa tace "momy tace ki rakani dakin yayanki" rukayya bata ce komae ba ta nufi sama don kai ta dakin Ashnaah na biye da ita a baya, suna haurawa sama ta nuna mata Dakin Khaleel, Ashnaah ta murda kofar ta bude ta shiga abunta, yana xaune kan gado ya dafe kansa, ya dago da sauri don ganin wanda ya shigo fuskarsa a daure, ta ajiye masa abincin nn bakin kofa ta fice abunta ta koma Dakin ummi, ummi dae bata ce mata komae ba Ashnaah ta xauna ta ci gaba da kallonta tana ba ummi lbrin ynda film din yake, ummi na ta sauraronta. Karfe sha daya saura bayan an gama film din ummi tace "baxa ki kwanta ba Fateemah dare fa yyi" Ashnaah da har ta fara gyangyadi nn xaunen tace "xan kwanta momy" ummi ta kira Rukayya tace ta dauko ma Ashnaah kaya Mara nauyi tasa ta kwanta, rukayya ta dauko mata wani sabon kayan baccinta ta bata, Ashnaah ta karba ummi tace "to tashi ki tafi bayi ki canxa ko" Ashnaah tace "to" snn ta mike ta shiga bathroom ta sa kayan baccin snn ta linke kayan da ta cire ta maida hijab dinta har kasa ta fito. Xaune ta samu Khaleel a dakin, ta hade rae ta xauna inda take abunta, Ashnaah xata kwanta nn inda take a xaune ummi tace "ki tafi can dakin ki kwanta mana Fateemah" ta yi shiru bata ce komae ba amma ranta Bae so ba, can dae tace "to" snn ta mike tace sae da safe ta fice daga dakin ta nufi dakin Rukayya ta dan bude ta ga har ta kashe wuta abunta, tsaki tayi ta nufi dakin Khaleel ta bude a hankali ta shiga ta kwanta ta shige cikin bargo nn da nn bacci ya dauketa don dama baccin take ji" [10/10, 6:37 AM] ‪+234 701 117 6189‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 24...... karfe sha biyu saura Khaleel ya bude kofar dakinsa ya shigo ya kulle yana kallon Ashnaah dake bacci hankalinta kwance cikin bargo, ya tsaya daga nn bakin kofar yana kallonta da mamaki, can yyi murmushi ya gyada kansa alamar xaki gane kurenki snn ya nufi bathroom, wanka ya kuma yi ya fito daure da towel yana goge gashin kansa da karamar towel, bude wardrobe dinsa yyi ga ciro sleepn robe dinsa fari ya sa, wayarsa dake gaban madubi ya shiga kara ya karasa gaban madubin yana kallon screen din wayar, karan wayar ya farkar da Ashnaah ta bude fuskarta a hankali tana kallonsa, yana tsaye gaban madubin yana kallon wayar har ya katse snn ya kashe wayar gaba daya, Ashnaah ta maida kanta cikin bargo da sauri, bargo babba ya dauko cikin wardrobe ya shimfida a kasa snn ya karasa daya side din da Ashnaah take ya dauki pillow ya ajiye kan bargon snn ya kashe wutan dakin ya kunna bedside lamp, sae a snn Ashnaah ta kuma bude fuskarta ta ga ya nufi fridge ya bude da key ya ciro wata kwalba, ya xauna gefen gado can nesa da ita ya bude ya shiga shan abun sa, sae kallonsa Ashnaah take har daga karshe taga ya mike ya kulle kwalban ya mayar cikin fridge din ya dawo ya kuma xaunawa gefen gadon ya dafe kansa, Ashnaah dae sae lekansa take ta cikin bargo don wutan dakin na da duhu, juyawa taga yyi yana kallonta, nn da nn gabanta yyi mugun faduwa ta rumtse ido da sauri, ya dde yana kallonta daga karshe ta ga ya mike ya sauka kasa ya kwanta kan bargon da ya shimfida nn kasan, sae a snn hnklin Ashnaah ya kwanta, tana nn kwance har kusan daya na dare bacci ya ki xuwa mata ta mike xaune a hankali tana lekan khaleel taga ya juya ma gadon baya, fridge ta kalla a xuciyarta tace ko me ya sha a kwalba da yaki xubawa a kofi ae sae na gani, mikewa tayi a hankali ta cire bargon jikinta da hijab ta sakko kan gadon ta isa gun fridge din ta bude taji shi a rufe, ta bude baki da mmki to meye na wani rufe fridge, gaban madubinsa ta nufa a hankali ta ga ko wayarsa na gun, ta laluba ta samu wayoyinsa duka biyun a wajen, daukan daya tayi ta danna ta ji a kashe ta dauka dayan ta danna sae ga haske, fridge din ta nufa da wayar a hannunta ta duka tana haska fridge din ta ga ashe keyn ma na jiki, budewa tayi snn ta jawo fridge din a hankali, duk wnn abinda take Khaleel na kallonta, duk a xatonsa ruwa xata sha, ya ga ta fiddo da kwalban da ya maida ta shiga haska wayarsa jikin kwalban don karanta menene, Alcohol kadae idonta ya sauka kai taji an daka mata tsawa "keee" a tsorace ta sake kwalban hannunta ta mike tsaye jikinta na rawa, ba karamin tsorata tayi ba don bata taba tunanin idonsa biyu ba, ya mike tsaye da sauri ya nufi gun kwalban da ya tarwatse kasan dakin, Ashnaah ta nufi kofa da gudu don duk tunaninta kama ta xae yi, fixgota yyi ganin fita xata yi ta bare baki a tsorace xata fasa ihu ya juyota ya matse ta jikinsa ya rufe bakinta da hannunsa yace " nayi maki wani abu ne" kkrin cire hannunsa daga bakinta ta shiga yi amma ta kasa, tuni jikinta ya fara rawa ya jefata kan gado ya hau gadon shima yana kallon fuskarta cikin dim light din dakin, kkrin sauka ta shiga yi da sauri, yyi saurin fixgota ta fado jikinsa, kan tace komae ya rufe bakinta da hannunsa ya matse ta jikinsa, yana kallon fuskarta cikin dim light din dakin yace "kika ce baki da banbanci da budurwar dake gidan iyayenta ynxu ko?" Ashnaah ta shiga kallonsa a tsorace tace "ni? Yaushe na fadi hka?" [10/10, 6:41 AM] ‪+234 701 117 6189‬: ~Dr khaleel~ By khaleesat Haiydar 25..... khaleel yyi murmushi ya kashe bedside lamp din dakin har lkcn yana tana jikinsa ya dago kanta yana kallon fuskarta yace "yhu re asking me ryt?" Ashnaah ta saki kuka ta shiga turasa tana cewa "don Allah kayi hkuri ni ba da kai nake ba fa" ya shaketa yace "kika sake tura ni sae na maki abinda baki yi xata ba, just stay calm idan ba hka ba yhu will regret it" kallonsa kawae take xuciyarta na bugawa, to me xae mata, rigar ta taga ya soma cirewa, ta rike hannunsa a tsorace cikin kuka tace "don Allah don Annabi kayi hkuri, kar ka min hka ka ga ni yarinya ce wayyo Allah na" dariya ssae ta basa, yace "ohw I c, ke yarinya ce ko?" cikin kuka tace "eh wllh am just 17" yace "to xan nuna maki ke ba yarinya bace" bata jira ya rufe baki ba ta fashe da wani kukan tana cewa "don Allah fa na ce maka kayi hkuri, wllh ni yarinya ce karama" ya dago kanta yana kallon for fuskarta da yyi shabe shabe da hawaye yace "ke yarinya ce kika iya daga hannu ki mari namiji" ta girgixa masa kai da sauri cikin kuka tace "kayi hkuri ban san xan mare ka ba, sharrin shaidan ne, kuma ae kai ma ka rama ranan" ya dauke fuskarsa don ta basa dariya ssae, ta shiga komawa baya a hankali, mikewa yyi ya sauko daga kan gadon ya fixgota kasa ya nufi bathroom da ita ya jefata ciki yace "kin ci sa'a ban ga abun burgewa a kwailan jikin nn na ki ba, in nace xan maki abinda ke raina ynxu ma sae dae in ba kaina wahala in cuce kai na, da yau kin gane kuranki don sae kin gwammace kida da karatu, mum dita kuma da kika ki gaisarwa daxu in mun je gida xa ki ban dalilinki nayin hka, wawiya kawae, ashe ke karamar yar iska ce tunda kika iya bude baki ki ba mutum hkuri, kinga gun kwananki yau don baki kai matsayin kwana cikin daki na ba" kallonsa kawae take kmr munafuka tsaye a bathroom din, ya rufe kofar daga waje ya sa key, Ashnaah tayi murmushi tana gyada kai a xuciyarta tace "xaka gane baka da wayo" bata damu da bathroom din da ya shigo da ita ba tayi xamanta abunta ta Jingina jikin tiles din dakin kalamansa na mata yawo a ka. har asuba Ashnaah bata yi baccin kirki ba a bathroom din, bude kofar bayin da aka yi yasa ta mike tsaye da sauri ganinsa tsaye bakin kofa, fixgota yyi ya wurgota waje ya shige bathroom din don yin alwala, ta nufi kofar dakin da sauri ta murda ta ji sa a rufe, ba karamin haushi hkn ya bata ba, tana nn tsaye ya fito daga bayi, ya nufi kofa yana kallonta yace "oh fita xa ki yi, to fita don Allah" hanya ta basa bata ce komae ba, yyi kwafa ya bude kofar da key ya fice don xuwa masallaci, gajiya tayi da tsayuwa ta nufi bathroom din ita ma tayi alwala ta fito ta sa hijab dinta ta tada sllh, har gari ya fara haske bata mike daga gun da tayi sllh ba ga wani bacci da take ji, kwanciya tayi nn kan darduman nn da nn bacci ya dauketa, can kusan karfe takwas ta farka ta mike xaune da sauri tana kallon agogo, kamshin sabulu da taji ya gauraye dakin yasa ta gane ana wanka a bathroom, ta mike tsaye ta nufi kofa a hankali ta bude ta fice daga Dakin ta nufi dakin Ummi, bata samu Ummi a dakin ba, hkn yasa ta shiga bathroom dinta ta wanke bakinta da mouth freshener kawae, ta wanke fuskarta snn ta fita ta fita daga dakin ta sauka downstairs jin kamshin soye soye, kitchen ta nufa ta same ummi da Rukayya suna hada break fst, ta gaida ummi cikin ladabi ummi ta amsa da fara'arta tace "an tashi lfya" Ashnaah tayi murmushi kawae, rukayya ta gaida ta ba tare da ta kalleta ba, Ashnaah ta amsa snn ta karasa cikin kitchen din don taya su, ummi tace "haba dae tafi kiyi xaman ki kawae ae mun kusa gamawa" Ashnaah tace "aa xan taya ku momy" ummi bata kuma ce mata komae ba ta shiga taya su juya potatoes din dake cikin mai kan gas. karfe goma Khaleel ya shiga dakin mum dinsa ya xauna yana kallon Ashnaah dake kallo yace "ke fa nake jira na ga kuma ba ki shirya va" Ashnaah na masa wani irin tace "ina xa mu" ya dake yace "gida" ta dan tabe baki tace "ni dae ina nn, ko ba ca kayi sati xan ma momy ba" Khaleel ya dubi mum dinsa da ke danna waya ya rasa me xae ce, Ummi ta ajiye wayarta tana kallon Ashnaah tace "Fateemah ki bari in kin kwana biyu sae ya kawo ki kiyi adadin kwanan da kike so a nn, kinga Bae kamata bakya dakin ki ba ynxu, kuma akwae masu xuwa ganin daki, ki bari sae an kwan biyu sae ki xo nn ko da kanki ma" Ashnaah ta dauke kanta ta hade rae bata ce komae ba, Khaleel ya mike ya fita daga dakin, ummi tace to tashi ki shirya ki wuce, bata mata musu ba ta mike ta sa hijab dinta kawae ta koma ta xauna, Khaleel ya dawo dakin rike da car key dinsa, yyi ma umminsa sallama yana kallon Ashnaah yace "mu je" mikewa tayi ita ma tayi ma ummi sallama fuskarta dae a daure ta fice daga dakin, bayan mota ta shige abunta ta daga ma su Ummi dake daga mata hannu, hannu ita ma, Khaleel dae Bae ce komae ba ya bude driver seat ya shiga ya tada motar suka bar gidan, sae da suka bar anguwar snn yyi parkin ya juya yana mata mugun kallo yace "ke ance maki ni driven ki ne da xa ki jabe min a bayan mota" tace "warce ka saka gaba jiya ka kuma dauketa ka sa ta gaba ni kam ga maxaunina" ya bude mota a fusace ya fito ita ma ta fito da sauri ta daya bangaren tana hararansa tace "wllh ka taba ni sae na rama, in kuma karya ne ka gwada ka gani" tsayawa kallonta yyi, ta tabe baki ta dauke kanta tana rike da kugunta tana girgixa Kafa, ya dauke kai yyi murmushi ya koma seat dinsa ya shiga ya xauna, snn ta ja tsaki ta nufi front seat ta bude ta shiga ya ja motar suka bar wajen. 26...... Dae dae wani babban clinic taga yyi park, ta dan sace kallonsa taga wayarsa yake dannawa, can ya kara a kunne yace "kina clinic ne" Ashnaah ta tabe baki a xuciyarta tace kanka ake ji, murmushi ta ga yyi yace "not so wllh, ynxu dae ki fito ina waje" yana kai wa nn ya kashe kiran ya ajiye wayar nn gefensa, ba a dau lkci ba Ameesha ta fito daga gate din hsptl din, ya tsura mata ido tana takowa a hankali, duk ta rame ta xama wani iri sae ta basa tausayi ssae, ya shafa kansa har ta karaso gun da yake, ya xuge glass din motar yana kallon ta, hawaye ne cike idonta, ya bude motar ya fito yana kallon kyakkyawan fuskarta a hankali yace "y those tears" kuka ta saki ya kauda kansa kawae xuciyarsa na tafarfasa, shi Bae san ynda xae yi da Ameesha ba, shi ba sonta yake ba gwara dae wani lkcn ya kan ji sha'awarta, yasan Ameesha kyakkyawa ce ssae bata da wata makusa a jikinta, but kawae shi dae har yau Bae ga macen da xata burgesa ya so ta ba, Ashnaah kam sae kallonsu take da mamaki daga cikin motar, to wacece kuma wnn gantalalliyar da tasa namiji a gaba tana kuka, ita dariya ma abun ya bata kmr ta fito tayi kallon da kyau, Khaleel ya juyo yana kallon Ameesha ya karaso gabanta ya rungumota jikinsa a hankali yace "kiyi hkuri Ameesha, am sorry" dago kanta yyi yana share hawayen fuskarta yace "don't wrry kin kusa mallakana a matsayin mijin ki kmr ynda kike buri a ko da yaushe I promise yhu dat" bata dago kanta ba bare tace komai, ya riko hannunta cikin nasa yace "xa ki raka ni gida ne ynxu," ta dago kai tana kallonsa tace "matar ka fa" ya hade rae yace "ca nayi maki ina da mata, maid dina dae xaki ce ko kuma Kice mistress duk da ban ma bata wnn matsayin va tukun." Ameesha tayi shiru tana kallonsa ya gyada mata kai yace "yes ga ta ma a mota, in xaki bi ni gida, ta fito ta baki front seat mu tafi" Ameesha ta kalli motar da sauri suka hada ido da Ashnaah dake kallonta, gabanta yyi mugun faduwa tana kallon Ashnaah tace "ina yini" Ashnaah tayi dariya hade da tabe baki tace "ke kuma irin kaddararrki knn," sae kuma ta fashe da dariya tace "Allah ya sauwake maki, amma kuma fa kin ban mmki duk kyan nn naki ki rasa wanda xaki so a duniya sae wnn abun dake gaban ki" Ashnaah ta kuma fashewa da dariya duk da ba karamin faduwa gabanta yake ba, ta nuna Khaleel tace "har ina abun so a nn, ae wllh ko maxa sun kare a duniya bn ga abun da xanyi da wnn mutumin ba, tab sae kace uwata ta min baki" [10/10, 6:42 AM] ‪+234 701 117 6189‬: ~Dr Khaleel ~ By Khaleesat Haiydar 27...... Khaleel ya juya a hnkli yana kallon Ashnaah da mugun mmki, ta galla masa harara ta tabe baki ta dauke kanta xuciyarta na ci gaba da bugu, Ameesha kam kallon Khaleel kawae ta tsaya yi, turata yyi da karfi daga gabansa a fusace ya nufi driver seat ya bude ya shiga ya tada motar yyi reverse ya bar layin da gudu, Ashnaah dae sae faduwa gabanta yake barin ynda ta ga yana gudu, da kyar ta juya tana kallonsa ta dake ta hade rae tace "gida wae xa mu tafi ynxu" Bae tanka ta ba sae gudu kawae yake da mota, nn fa hnklinta yyi mugun tashi, ta marairaice masa tace "ka min mgna mana gida xa mu?" Parkin taga yyi kan ta ankara ya wani irin fixgota ya shiga marin ta, gigicewa tayi ta fasa kuka tana cewa "wayyo Abbana na shiga uku me nayi maka" ihu ta dinga yi ganin yaki kyaleta ta shiga basa hkuri tana rusa kuka, turata yyi da karfi ta bugu da mota snn ya ci gaba da tukinsa, Ashnaah ta dinga kuka a motar tana rike da kanta tana kiran momynta, yana isa gida yyi parkin bayan mai gadi ya bude masa gate, snn ya bude mota ya fito ya xaga ta inda take yana huci ya bude kofa ya fixgota ya nufi cikin gida da ita, kuka take tana rokansa Allah da annabi yyi hkuri amma Bae ma san tana yi ba, ya bude falon ya jefata ciki ta Mike da sauri jikinta na rawa xata gudu yyi saurin fincikota ya kai mata wani wawan marin kuma, rungumesa tayi ta boye fuskarta a kirjinsa cikin kuka tana cewa "don Allah don annabi ka daina dukana wllh baxan sake ba kayi hkuri plss" fixgeta yyi daga jikinsa ya nufi sama da ita yana janta tana kuka tana rokonsa, dakinta ya bude ya jefata ciki har sae da ta bugu da gado snn ya rufe dakin ya bude dakinsa ya shige, kuka ssae Ashnaah take tana rike da kanta da take jin kmr ba nata ba duk jikinta ya mutu sbda axaba, baccin wahala ne ya dauketa nn kasan tiles din da take a kwance. Sae kusan la'asar ta farka ta mike xaune da kyar duk jikinta ciwo suke mata ga wani mugun ciwon da kanta yake, da kyar ta dafa gado xata mike taji jiri na neman kwasheta, ta koma ta xauna tana rera kuka a hankali tayi Mae isarta snn ta daure ta tashi tsaye tana daddafa bango ta shiga bayi don yin alwala don ko Azahar bata yi ba, a daddafe ta idar da sllh ta koma gado da kyar ta kwanta nan da nn bacci ya kuma dauketa. Bude kofar ta da taji anyi yasa ta farka a tsorace ta mike xaune taga wae ashe har dare yyi, tayi saurin mayar da kallonta ga kofar don gnin wnda xae shigo, ba karamin faduwa gabanta yyi ba ganinsa, kallo daya yyi mata ya dauke kai ya ajiye ledan hannunsa ya fice daga dakin, ta fashe da kukan takaici kmr xata hadiye xuciya, sae da taji ya shiga dakinsa snn ta soma cewa "wllh ka xo ka dauke gantalallen ledan ka mugu kawae axxalumi, kuma Allah ya Isar min" ta fada kan gado ta fashe da wani matsanancin kuka tana rike da kanta, wani mugun tsanan khaleel take a xuciyarta, ta kusa minti talatin tana kuka snn ta mike tsaye da kyar ta nufi bayi don yin alwala, ta dde xaune kan darduma bayan ta idar da sllhn daga karshe dae ta rarrafa don bata jin xata iya tashi don xaxxabi taji ke neman rufe ta, ledan da ya ajiye mata ta jawo ta bude ta ga take away na fried rice da salad ne sae naman kaxa da hollandia drink Mae sanyi, daya ledan kuma fruits ne, ball tayi da ledan da hannunta don takaici, nn da nn taji karfi ya xo mata ta mike tsaye da sauri ta dauki ledan ta bude kofarta a hnkli ta nufi kofar dakinsa ta bude take away din ta xaxxage shinkafar nn bakin kofarsa snn ta bude drink din ta tuttula kan shinkafar ta barbaxa fruits din nn bakin kofar kan shinkafar snn ta koma dakinta tayi kwanciyarta duk da irin faduwar da gabanta yake, duk ta rasa sukuni kwanciyar ma ya gagareta sae faduwa gabanta yake ssae, ta mike xaune can kuma ta nufi kofar bayi ta tsaya, bayan kusan minti talatin taji ya bude kofar dakinsa, ji tayi kmr xuciyarta xae shige cikinta don tsoro, ta shige bayinta da sauri jikinta na rawa, jira kawae take ta ga ya bude kofar dakinta amma shiru ta kusa wani minti talatin din a tsaye amma bata ga alamar xa a bude kofar dakinta ba, hamma tayi jin cikinta na kugi ta shiga bayi don sake alwala ta xo tayi isha, har ta idar da isha bata ga ya shigo dakinta ba sae ma ji da tayi ya bude dakinsa ya shiga, tayi tsaki ta mike ta nufi gado ta kwanta tace "da ka shigo dakin nn da ka sha mamaki na wllh" har kusan sha daya Ashnaah bata kuma jin motsin Khaleel ba, yunwan cikinta ya isheta bbu abinda take sae Hamma sae juye juye take kan gado, rabonta da abinci tun break din da tayi da safe, juyawa tayi ta rufe idonta ko bacci xae dauketa amma bacci ya ki xuwa har kusan karfe daya, ganin ba sarki sae Allah yasa ta mike xaune tana tunanin to ina xata samu abun da xata ci ynxu, mikewa tayi tsaye ta nufi kofa a hankali ta bude ta fito tana kallon bakin kofar dakin Khaleel, duk ya kwashe abincin da ta walakanta nn bakin kofar ya goge wajen, ta dan yi tsaki ta shiga sauka kasa a hankali don xuwa kitchen ta ga ko xata samu abin da xata ci, duk an kashe wutan ko ina har kitchen din, ta shiga lalube lalube har ta isa kitchen din snn ta bude ta shiga, ta fara laluba bango don neman switch din wutan kitchen din, kunnawa tayi farin wuta ya haska kitchen din ta shiga bin sa da kallo, take away ta gani a rufe da Rabin hollandia a glass cup, ta karasa da sauri ta bude taga jollof ne da nama a ciki an taba kadan an bari ga spoon ma a ciki, tayi murmushi ta sauko da shi kasa ta ajiye da drink din snn ta kashe wutan kitchen din ta xauna nn kasa tana shiga ci da sauri da sauri. [10/10, 6:42 AM] ‪+234 701 117 6189‬: ~Dr Khaleel ~ By Khaleesat Haiydar 28..... Ashnaah ta juya da sauri tana kallon bayanta a tsorace, sae taji kmr motsi a falo, ta dde tana kallon bayanta daga karshe ta ci gaba da cin abincin gabanta da sauri cikin duhun, haske ta ga ya gauraye kitchen din ta daga kai da sauri suka yi ido hudu da Khaleel, yana tsaye daga bakin kofar sanye da 3qtr da singlet, ji tayi kmr ta nutse wajen don kunya, ta tsunkuyar da kanta ta mike tsaye kmr munafuka ta juya masa baya, kallonta kawae yake daga sama xuwa kasa yana murmushi, can dae ta durkusa da sauri ta dauke abincin da drink fuskarta a daure ta ajiye gun sink din kitchen din ta wanke hannunta ta nufi kofa ba tare da ta kallesa ba ta raba ta gefensa da sauri xata fita, ya fixgota yana Mata wani irin kallo yace "koma ki cinye shi" hade rae tayi tana hararansa tace "ca nayi maka yunwa ,nake..." Shiru tayi ganin irin kallon da yake mata, ta yi kmr xata yi kuka tace "ni ba yunwa nake ji ba" fincikota yyi suka shiga kitchen din ya sauko da abincin ya ajiye nn kasa yace "sae kin cinye shi wllh" nn da nn hawaye ya cika idonta ta ce "ni baxan ci ba" sae kuma ta fashe da kuka, ya fixgota ya juyo da ita yana mata mugun kallo yace "kuka kike min"share hawayenta ta shiga yi ta durkusa gaban abincin ta shiga ci a hankali yana kallonta, har sae da ta cinye don dama kadan ya rage snn ta mike fuskarta daure, xata fita ya kuma fixgota yace "wa kika bar ma drink din" Bae jira me xata ce ba ya dauko ya mika mata fuskarsa daure, ta dake ta karba daga hannunsa ta juya masa baya ta shanye snn ta ajiye ta fice daga kitchen din da sauri har tana neman bangaje shi, ya daka mata tsawa, ta juya tana kallonsa fuskarta daure, yace "xa ki kuma shan wani dukan ne ynxu idan baki yi hnkli ba yarinya," tana masa mugun kallo tace lallae ma, da yake ca aka yi maka yar ka ce ni va, wllh ka kuma taba ni na rantse da Allah sae na rama" tsayawa kallonta yyi can ya dauke kansa yana murmushi, ta hararesa duk da gabanta faduwa yake ta juya da sauri ta nufi stairs, ya bi bayanta ta saka gudu tana kiran momynta, sae da ta hau stairs na biyar snn ya risketa, ya fincikota ta fado kansa, ta juya da sauri ta kankamesa jikinta na rawa tace "wayyo ba da kai nake ba don Allah" Bae tanka ta ba ya shiga janta suka haura sama har lkcn ta ki sake shi ta boye fuskarta a kirjinsa, ya bude falonsa ya shiga ya kulle,snn ya nufe bedroom dinsa nn ma ya kulle bayan sun shiga, hkn yasa ta daga kai da sauri don ganin inda ya shigo da ita, ba shiri ta sakesa, ta koma baya tana kalle kalle kmr xata yi kuka tace "kayi hkuri ni ba da kai nake ba fa" wardrobe dinsa ya nufa ya bude ya shiga fiffito da duka jallabiyansa da ba guga, ya dauke su gaba daya ya ajiye su kan rug din dakin ya fito da dutsen guga ya ajiye snn ya nuna mata pressing board yace "ki tabbatar kin goge min su tsaf" bude baki tayi tana kallonsa, wardrobe ya kuma budewa ya kwaso cover shoe dinsa kusan kala biyar ya xube su nn kasa, snn ya fito da Polish da brush ya ajiye kusa da su snn ya mike yana kallonta yace "yhu make sure u Polish dis also, more especially dis dan gobe da shi xan fita aiki" Ashnaah ta fashe da dariya kmr wata tababba ta xube kasan dakin har da rike ciki tana kyalkyala dariya, ya dauke kai don shi ma ta basa dariyan, can ya juyo ganin taki daina dariyan ya nufi gun da belts dinsa suke ya dauko daya yana mata wani irin kallo yace "its funny ryt" mikewa tayi da sauri nn da nn tayi tsit ta nutsu tana kallonsa, yace "ci gaba mana" tace "ni fa bn iya guga va shi yasa nake dariya wllh" yace "ko, to bari in koya maki" daga belt ta ga yyi xae tsula mata tana ganin hka ta yi kansa a tsorace ta fada jikinsa ta rungumesa ta rike belt din, duk ynda Khaleel ya so regainin balance dinsa Kasawa yyi duk suka fada kan gado, ya turata daga jikinsa da sauri xae mike ta fixgosa ya kuma fadowa kanta jikinta na rawa tace "wllh na iya xan yi don Allah kar ka dokeni" da kyar ya iya turata kuma ta fada kan gadon kan ta kuma fizgosa ya mike ya nufi bathroom da sauri, ta mike xaune ta bisa da kallo gabanta na ci gaba da faduwa, mikewa tayi ta nufi kofa ta bude ta fice daga dakin. ~Dr Khaleel ~ By Khaleesat Haiydar 29..... Washegari da safe Ashnaah na xaune gaban madubi daure da towel ta fito daga wanka taji fitar motar Khaleel, ta karasa window da sauri tana kallon motar har ya fice daga gate mai gadi ya kulle gate din, da sauri ta nufi kofarta don sauka kasa ta ga ko ya kulle kitchen din yau ma ae ko da ya ca cuceta don tun asuba cikinta ke kugi, da sauri da sauri ta nufi kitchen din suka kusan cin karo bakin kofar kitchen din ta rike towel dinta ta koma baya a tsorace tana kallonsa, sae take ga kmr ba shi bane, dauke kansa yyi da sauri ya juya mata baya, juyowa ya kuma yi ya bi ta gefenta va tare da ya kalleta ba ya fice daga kitchen din, ta bi sa da kallon mmki har ya isa stairs snn ta fashe da dariya, to ko dae tsoronta ya fara yi ne, ta kuma kyalkyalewa da dariya snn ta shiga kitchen din tana kallon cup din da ke ajiye da ruwan xafi a ciki da alamar tea xae hada, drawers din da ta gani ta shiga bubbudewa don neman kayan tea, duk ta samu har da sugar da lipton, ta fiffido su ta ajiye gefe snn ta dauki cup da spoon, ta kinkimesu gaba daya ta nufi dakinta da su, ta jera su nn kan side drawer dinta snn ta kuma sauka, ta nufi kitchen din ta dauki electric kettle din da ta gani ta karasa dinnin ta kuma daukan bread din da ke kai ta koma sama ta kulle dakinta, tana saka kaya taji budewan gate da shigowar mota, ta karasa window da sauri taga anyi parkin motar nn tsakiyar compound, sae kallo take ta ga wanda xae fito, wani mutumi ta gani, ta dan yi tsaki ta koma ta ci gaba da abinda take aka danna kararrawar gidan, tana ji Khaleel ya bude dakinsa ya sauka kasa, bayan kmr minti biyar ta kuma leka window ta gansa tsaye jikin motar yana waya, farar t-shirts ne jikinsa da bakar wando da ganinsa kasan aiki xae fita, bude motar yyi bayan ya gama wayar ya shiga, mai gadi ya bude masa gate, Ashnaah tayi tsaki ta koma ta ci gaba da abinda take. Khaleel na xaune office yana flipping thru files din dake gabansa, ko kadan hnklinsa baya kan abinda yake, ya rasa takamai mai wani tunani yake a xuciyarsa, Ashnaah ce ta fado masa ya tura files din gabansa kawae ya sauke ajiyar xuciya a hnkli yace "yes na gano abinda ke damuna ynxu," mgnr xuciya ya shiga yi "just tired of dis forsaken gal I guess, an obstacle 2 my life, yes a great one, den wat am I still waiting 4, y nt take my revenge and let her go" bude kofar office dinsa da aka yi yasa ya dago kansa da sauri, Ameesha ta shigo office din da sallamarta, yyi huci me xafi yana nuna mata kofa yace "get out please, just lemme b for heaven sake" juyawa tayi a hankali ta fita daga office din ta kullo masa, tsaki yyi ya jinginar da kansa jikin kujerar da yake xaune, bayan kmr minti goma a ka kuma bude kofar ya mike tsaye a fusace duk a tunaninsa ita ce, Najeeb ne ya shigo, khaleel ya sauke ajiyar xuciya ya koma ya xauna, Najeeb ya xauna kan table din abokin nasa yana masa wani irin kallo sae kuma ya fashe da dariya yace "Ango ka sha kamshi sae yau aka yi resuming," bnxa khaleel yyi masa ya shiga signin files din gabansa, Najeeb yyi yar dariya yace "ka bamu mmki Khaleel dama duk cika baki kke ashe, kasa mun xuba ido...." khaleel ya Mike da sauri ya katse sa yana kallonsa yace "enuf plss, just watch n c" Duk da irin ynda gaban Ashnaah ke faduwa hkn Bae hanata abinda take ba, tsaf ta fiddo gaba daya alcoholic drinks din da ta gani fridge dinsa tana tabe baki tace "no wonder ashe mashayin giya ne dae" kofa ta ji an bude downstairs, xuciyarta ya kusa shige wa cikinta bata kuma wani tunani va ta fice da gudu daga dakinsa jikinta na rawa, Meenah ta hango tsaye falo tana kare ma falon kallo, Ashnaah ta sauke ajiyar xuciya ta dafe kirjinta dake bugawa da karfi har lkcn, kasa ta sauko tana ma Meenah wani irin kallo tace "ya xa ki shigo ma mutane gida va sallama" Meenah tace "na ga dae ba gidan ubanki bne nn din ko" Ashnaah ta xaro ido tace "ubana kuma" Meenah tace "hka dae na gani" karasowa gabanta Ashnaah tayi a fusace wae xata mareta, dae dae nn khaleel ya shigo falon, Ashnaah ta xaro ido a tsorace tana kallonsa tunawa da tayi bata mayar Mae da abubuwan sa ta fito da ba daga fridge, ihu ta saki ta dafe kuncinta tana kallon Meenah tace "kika mare ni" sae kuma ta fashe da kuka har da durkusawa, Khaleel ya karaso yana kallon Meenah dake kallon Ashnaah da mmki yace me ya shigo da ke gidana, mikewa Ashnaah tayi da gudu ta nufi sama don xuwa ta mayar da abinda ta fiffito da. [10/10, 6:42 AM] ‪+234 701 117 6189‬: ~Dr Khaleel ~ By Khaleesat Haiydar 30..... Khaleel ya bi Ashnaah da kallo har ta haura sama snn ya juya yana kallon Meenah, da kmr xae yi mgna sae kuma ya fasa ya nuna mata kofa fuskarsa a daure alamar ta fita, juyawa tayi abunta ta fice daga falon, snn ya nufi sama, dae dae bakin kofarsa suka kusa cin karo da Ashnaah ta fito daga falon nasa, ya tsaya kallonta da mmki yace "wat? Me kike nema a nn" ta xaro ido tace "aa ni ba shiga fa nayi ba" bin ta yyi da kallo ta karasa dakin ta da sauri har tana tuntube ta shige, ya shiga nasa falon yana bin ko ina da kallo ko xae gano me tayi amma bae ga komae ba, ya nufi bedroom dinsa nn ma hka yyi amma bae ga alaman an shigo ba ma, xama yyi a hankali Murya can ciki yace "M abou completin Ma mission nd lettn go of her very soon" mikewa yyi kmr Mara laka ya nufi bathroom. Yau Sunday Khaleel na kwance dakinsa idonsa lumshe kmr me bacci aka danna bell din gidan, ya mike xaune da sauri yana tunanin waye xae xo masa a wnn tym din da yake hutawa, wayarsa dake gefensa ya shiga ring ya Duba ya ga no din amininsa al-ameen, dagawa yyi Al-ameen yace masa gashi a bakin kofa, Khaleel yyi shiru yana kallon wayar, mikewa yyi a hankali ya dauki jallabiyarsa ya saka yana tunanin yaushe childhood frnd dinsa ya shigo kaduna bae sani ba, murmushi yyi ya nufi kofa ya fita ya sauko downstairs, ko ba a gaya masa ba yasan Ashnaah na kitchen jin kamshin girki da ya gauraye falon, ya nufi kitchen din ya tsaya daga bakin kofa yana mata mugun kallo, yar rigar bacci ne iya gwiwa jikinta, tana tsaye kusa da gas tana juya indominta, tana ganinsa ta juya masa baya da sauri, ya dake yace "xo ki fita" ta juya tana kallonsa tace "to sae in bar abincina ya kone" a fusace ya karaso kitchen din ya kashe gas din snn ya turata waje ya rufe kitchen dinsa, kallonsa take kmr xata shakesa tana huci, ya nuna mata stairs fuskarsa a daure yace "bar min falo na" ganin ynda ya hade rae yasa ta nufi sama kmr xata tashi sama, kofar falon ya nufa ya bude murmushi dauke fuskarsa , amininsa ya gani tsaye da matarsa da boyz dinsu guda biyu, da mmki ya wara idonsa yace "waw irin wnn surprise visit din frnd, bismillanku madam" matar tayi murmushi suka shigo falon gaba daya, Khaleel na rike da boyz din, Al-ameen yace "naga kai Baka da niyyar xuwa inda nake shi yasa ni nace bari inyi sacrificing rana daya in xo, wae ace duk ynda muke da kai Ibrahim kayi aure ba tare da sani na ba, me nayi maka hka, ynxu dae a takaice yhu re tryn 2 tel me Baka yi da ni da su Najeeb kke yi ko? Those silly frndz of urs da suka yi corruptin din ka" Khaleel yyi dariya yace "but wa yace maka nayi aure?" Al-ameen yyi tsaki ya nemi waje ya xauna yace "ka dae kyauta Khaleel, ynxu ina amaryar take ita muka xo gani da madam" khaleel ya dan kirkiri murmushi yace "tana sama bari in kirata" da kyar ya mike daga xaunen da yake ya nufi sama. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 31..... Khaleel ya dde tsaye bakin kofar Ashnaah yana tunanin me xae ce mata idan ya shiga, tura kofar yyi ya shiga dakin, yana bin ko ina da kallo, karar ruwa da kamshin sabulun da ya ji yasa ya gane wanka take, ya dan yi tsaki ya ja stool din dake gaban madubinta ya xauna yana kallon kayan tean sa da ta jera kan bedside drawer dinta, yyi murmushi ya kauda Kansa, ya kusa minti biyar a zaune ta fito daure da towel tana goge gashin kanta da towel karami, a tsorace ta koma baya tana kallonsa, ya dauke kansa ya mike tsaye, ita kuma ta nufi gado da sauri ta dauki hijab dinta ta saka, sae a snn ya juya yana kallonta xae yi mgna ta Riga sa,"Haba don Allah, ya xaka shigo ma mutane daki ba sallama, ynxu da bbu tawul a jikina fa" tsayawa kallonta yyi ta galla masa harara, ya dauke kai yana dan murmushi snn ya kuma juyowa yana kallonta yace "ke har kina da abun boyewa a jikin ki? Me xaki boye a nn" tace "eh din, ko ma dae me nake boyewa wnn ba matsalar ka bace," tsaki yyi yace "idan kin ga dama ki sakko gaida frnd dina, nd mind yhu, kika kuskura kika yi misbehavin na lahira ma sae ya fi ki jin ddi, just calmly go dia do wat u re suppose 2 nd leave" wani kallon bnxa take masa snn tace "wnn ne kuma Baka isa ba don ni ba matarka bace wllh," kallonta ya tsaya yi xuciyarsa na tafarfasa, tayi tsaki ta karasa wardrobe dinta ta bude xata dauki kayan da xata sa tana Satan kallonsa da gefen ido don duk a tsorace take, gani tayi ya yo kanta ta fasa ihu a tsorace tace "wllh wasa nake xan tafi fa" ya karaso gabanta kan ta gudu ya fixgota ta fado jikinsa ya juyo ta yana kallonta, ta marairaice tace "don Allah kayi hkuri wasa nake fa xan je wllh" cikin idonta yake kallo, ta sauke idonta da sauri ya sake ta, ya juya ya fice daga dakin, ta bi sa da harara snn tace "xa ka gane kuran ka" riga da skirt dinta ta sa bayan ta shafa mai snn ta dan gyara fuskarta, ta dauki dankwalin kayan ta daura snn ta sa flat shoe dinta me kyau kalan atamfar jikinta ta sa, ta feshe jikinta da turare snn ta fito ta sauko falo, da fara'arta ta tare Al-ameen da matarsa, sae tsokanan Khaleel Maryam matar al ameen take wae ya samo balarabiya ya aura, Shi dae Khaleel sae kirkiran murmushi yake, Ashnaah tace "wae kuma fa Anty a hka yake cewa ya fi ni kyau fa" Maryam tayi dariya tana kallon mijinta tace "ka ji dear don Allah ka fadi gskya bata fi sa kyau ba, shi hske kadae ke cecensa fa" Ashnaah tace "atoh dae fada masa anty" Khaleel ya juya yana kallon Ashnaah, ta galla masa harara, ya dauke kansa yana murmushi, Al-ameen yace "a hka dae kika gansa kika ce sae shi" Ashnaah ta fashe da dariya tace "yace dae sae ni, Amma ni ina na san shi" kallonta Khaleel yake, ta kuma galla masa harara snn ta mike tace "bari in kawo maku drinks" sama ta nufa don bbu komae cikin fridge din dake kitchen da falo, tasan sbda ita yaki xuba komae cikin fridge din don kar tasha, shi kam bin ta yyi da kallo don bae san inda xata samo drinks din ta kawo ba, maganar da Al-ameen ke masa ne yasa ya mayar da hnklinsa kan abokin nasa, dakin Khaleel Ashnaah ta nufa don bbu komae fridge dinta ita ma, ko ruwa xata sha sae dae ta sha ba tap, kafin ta bude fridge din sae da ta fara leka bedroom dinsa, ko ina tsaf ga kamshi Mae ddi hade da sanyin Ac, ta dan tabe baki xata bar wajen sae ta hango wayoyinsa dake gaban madubi a kwance, ta karasa cikin dakin da sauri ta nufi gaban madubin ta dauki waya daya a xuciyarta tace bari in kira mum dina, da sauri ta gama dialing num din momynta ta shiga kira har ya katse bata daga ba, ta kuma kira ba a dauka ba tayi tunanin kila wayar na sama ita tana downstairs, har xata ajiye wayar ta tuna usman dinta da sauri shima tayi dialing no dinsa don tana da shi a ka ta kira ta ji a kashe, ta ja dogon tsaki har xata ajiye wayar ta tuna kawayenta na makaranta, tayi shiru tana nazarin ko xata iya tuna nmbr ummi kawarta don nmbrta bae da wahala, ta dae yi dailin nmbr tana tantaman hka ne ko ba hka bne, bugu uku a daga, tace "ummi ce don Allah" muryar ummi ta ji ta daya bangaren da mamaki tace "Ashnaah" Ashnaah tayi dariya tace ashe dae xa a dani, off head fa na kirkiri no dinki, wllh Baku da kirki ko ku nemeni ummi amma bbu damuwa, ummi tace "Allah sarki fateema kinsan sau nawa muke xuwa gidanku mama tace ita ma bata san gidan ki ba hka ma Ashfah, wllh bbu san inda xa mu same ki bne Ashnaah gashi ba mu da nmbrki, wnn ne Sabon nmbrki, ya amarci" Ashnaah ta tabe baki tace "ke dae bari, ynxu dae ki je gida ki ce ma Ashfah ta raka ki gidan Anty shafa, sae ki roketa ta kawo ku gidana ae ita ta san nn, ita kuma Ashfat ki ce mata ta kyauta ngd, kin ga sae anjima kar kuma fa ki kira Layin nn don na gantalallen ne, sae kun xo" Ashnaah na kai wa nn ta katse kiran ta goge duka nmbrs din da ta kira ta ajiye wayar ta fito da sauri falo ta bude fridge don daukan ma bakin Khaleel drinks, hollandia daya kadae ta gani sauran duk giya ce ta dan tabe baki har da xata dauki hollandian, sae kuma ta fasa tayi tsit kmr me naxari, murmushin mugunta tayi ta dauki wine din kwalba biyu ta fito ta sauka downstairs, tace "sannunku" snn ta nufi kitchen dan dauko faranti da cups ta daura wine din, Khaleel ya bi ta da kallon mamaki, bae san lkcn da ya mike ya bita kitchen din da sauri ba, ya samu har ta gama daura su kan faranti xata fito ya rikota da sauri yace "ke meye hka kike yi, me ya kai ki dakina" ta fixge hannunta tace "A'ah me nayi, daga na dauko ma bakin ka lemo shine nayi laifi" kuma rikota yyi da sauri ganin fita xata yi yace "kina da hankali kuwa" ta buge hannunsa tace "Allah xan maka ihu idan baka sakeni ba, to me xa su sha sun kwaso kishin ruwa" ganin da gske take yasa ya marairaice ya rungumota yace "pls listen ba lemo bne wnn wllh, ba ki ga hollandia a fridge din bne" tana kallonsa tace "to meye" ya hade rae yace "wnn kuma ba matsalarki bne" bude baki tayi tace "ohh hka ma xaka ce min ko to wllh sae na kai masu in ba lemo bne to meye guba ce ko me? Allah sae na kai masu don irinsu kadae na gani a gidan" Khaleel duk ya birkice mata yana rike da ita yace "stop it plss wllh ba lemu bne, tarnish din image dina kike son yi ko me" ta hade rae tace "to oya cika ni na ji" a hankali ya saketa, ta juya da gudu xata fice daga kitchen din ta kai yyi saurin rikota ya matse ta jikinsa ya kwashe kwalaban dake kwance kan farantin ya ajiye su cikin sink, sae kiciniyar kwace kanta take tana cewa ashe dae kasan abinda kke to wllh sae na kai masu, matseta yyi jikinsa ganin ynda take daga murya yasa ya rufe idonsa ya saka bakin sa cikin nata da sauri, still tayi ta xaro ido a tsorace tana kallonsa, sulalewa ya ga tana neman yi hkn yasa ya hadata da bango ya shiga mata wani kiss na fitan hnkli, kuka ta saki a tsorace tana turasa jikinta na rawa, sae taga kmr bae ma san tana yi ba. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 32..... Da kyar Ashnaah ta iya kwace kanta daga hannun Khaleel ganin yana neman kai su kasa ga zip din rigarta da ya soma xuge wa, mikewa tsaye tayi jikinta na rawa ta dauki dankwalinta da ya fadi kasa da sauri ta nufi kofa xata shiga falo, yyi saurin rikota ya mayar da ita jikin bangon, ta sulale kasa a tsorace ta toshe bakinta da hannunta gudun kar ta saki ihun da take shirin yi, hawaye na bin kuncinta, shi kam komawa yyi ya hade kai da bango ta daya side din, Ashnaah ta hade kanta da gwiwa ta shiga rera kuka, ya juya a hankali yana kallonta, idonsa ya kada yyi jajur hka ma lebbansa, mikewa Ashnaah ta kuma yi da sauri xata Kuma fita ya fixgota xata saka ihu ya bude kofar da xae sada ka da garden din gidan dake kitchen din ya turata waje ya rufe kofar, mayar da kansa yyi jikin bango yana mayar da numfashi, can dae ya dago bayan numfashinsa ya dai daita, ya juya a hankali ya jingina jikin bango yana tunanin ynda xae koma falo gun bakin sa ga shi bbu lemo, jikinsa ba laka ya nufi kofar da ya tura Ashnaah ya bude a hankali ya fita, Ashnaah ta Mike daga xaunen da take da sauri hawaye shabe shabe a fuskarta ta koma baya a tsorace, kallo daya yyi mata ya dauke kai ya nufi cikin gida gun mai gadi, xama yyi kan bencin da mai gadin ke xaune mai gadin na masa sannu da fitowo ya dan shafa kansa yace "lemo xaka je ka siyo min da ruwan gora Abdul, nayi baki bbu drinks a gidan, kayi amfani da kudin hannunka idan ka dawo xan Baka, kayi sauri don Allah xan jira ka a nn" cike da ladabi mai gadin ya amsa snn ya fita da sauri, bayan kmr Minti goma ya dawo rike da five alive guda biyu a Leda da table water biyu, Khaleel ya karba yyi masa gdya snn ya nufi back yard don shiga kitchen, Ashnaah na ganin sa ta kuma mikewa tsaye da sauri a tsorace, bae ko kalli inda take ba ya shiga kitchen din ya daura drink din daya da ruwa kan faranti snn ya nufi falo, suna ta hira abunsu Khaleel ya karaso falon ya ajiye drinks din hannunsa yana kirkiran murmushi yace "Sannun ku" Al-ameen yace "kai kuma daga ku kawo mana drink kae da matarka sae ku makale a kitchen, minti nawa xa muyi mu bar maku gidan ban da abin ku" Al- ameen ya karashe mgnr yana kallon Khaleel yana yar dariya Matarsa na taya sa, Khaleel ya ji kunya ssae amma ya waske yace "ka ji ka da wata magana daga na tsaya taya matata girki shine laifi, dariya Al ameen yyi yana kallon maryam yace "lallae kam mun ga alama girki ku ke." Shi dae Khaleel bae kuma cewa komae ba sae mikewa da yyi ya dauko boyz din abokin nasa yana tamvayarsu ajin da suke a sch, da kyar Ashnaah ta iya mikewa a hankali ta shigo kitchen, duk jikinta yyi sanyi ji take kmr har lkcn bakin sa na cikin nata, xakin bakinsa kawae ke mata yawo a nata, kasa shigowa falon tayi duk sae taji ma kunya take ji, dubara ya xo mata ta dauki indomin ta da ta dafa da safe ta saka shi a micro wave, sae da ya dumamu snn ta fiddo shi ta juye a plate ta bare eggs din da ta dafa ta daura kai snn ta dauki fork biyu ta sa a abincin ta gyara daurin dan kwalinta ta fito falon, dakewa tayi tana kirkiran murmushi tayi masu sannu da xama snn ta karaso falon ta ajiye abincin kan center table tana kallon yaran tace "ku xo ga abinci na dafa maku children" karasawa kujera tayi ta xauna tana kallon maryam da ke binta da kallo duk sae ta tsargu ta fara kame kame tace "Anty me xan girka maku, naga kar yaran su ji yunwa ne shi yasa na tsaya dafa masu indomie" Maryam tayi murmushi tace "haba dae yi xaman ki amarya yaushe muka karya da har xamu daura wani" Ashnaah tace "to Bari in bari xuwa anjima" ko kadan bata bari suka hada ido da Khaleel ba shi ma kuma hka don kin kallon inda take yyi, duk suka xama kmr wasu munafukai, kasa xama tayi a falon don duk sae ta jita a takure, ta mike tana kallon maryam tace "bari in je sama anty ina xuwa" Maryam tace "to sae kin sauko" karfe sha daya saura Al ameen yace xa su wuce, Khaleel yace "haba dae da wuri hka frnd ku tsaya kuyi lunch mana" Al ameen yace "ma yi a gidan mu, gwara mu Baku waje Yau Sunday ku huta da kyau, kira mana amarya muyi sallama" Sisters wata baiwar Allah ta kirani daxu wae ana sa nmbrta a karshen nvl din nn kuma sae ayi ta damunta da kira ana tsammanin ni ce, to ni kam gskya bn san Wanda ke editin ba yana sa nmbrta, don hka plss ba nmbrna bne ku bar kiranta bbu ddi hka nn, masu yi kuma Allah ya shiryesu Ameen. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 33..... Kwance Khaleel ya samu Ashnaah kan gado, tana ganinsa ta mike xaune da sauri ya hade rae ya dauke kai yace "ki fito kiyi masu sallama" bae jira me xata ce ba ya juya ya fice daga dakin, ta bi sa da wani kallon tsana, bedroom dinsa ya shiga, ba a dau lkci ba ya fito ya sauka kasa, bayan fitarsa da minti uku tayi tsaki ta mike ta sa hijab dinta ta sauko kasa, kin shigowa falon tayi ta tsaya daga bayan kujera tana masu sallama tana murmushi don gani take kmr sun ga abinda Khaleel ya mata a kitchen, tsaye ma ta samesu xa su fita, Al-ameen ya fiddo dubu goma ya ajiye gefen kujera yace "gashi amarya kiyi hkuri tunda mijin naki bae ga daman gayyata ta bikin ku ba, sae kuma wani lkci, idan kuma ya ga dama ya kawo ki inda muke to Alhmdllh" Ashnaah ta sunkuyar da kanta tana murmushi tace "Ae kam xan xo ko bae kai ni ba" Maryam tayi dariya tace "Da ko kin kyauta wllh" shi kam Khaleel bae ce komae ba ya durkusa gaban kidz din abokin nasa ya Ciro dubu biyar ya damka ma babban yace "gashi ku sha chocolate boyz, kar kuma ku ba dad din ku sae mum kun ji" dariya kawae yaran suka yi, Al ameen ya nufi kofa matarsa na biye da shi a baya yace "To Dr Khaleel mun xo mun yi xumunci sae kuma wani lkcn" Khaleel yyi murmushi yace "am so greatful frnd mu ma muna nn xuwa" Har waje bakin motarsu Khaleel ya raka su, Ashnaah kam kin fitowa tayi ta dauki kudin da Al ameen ya bata ta nufi sama, bayan kusan minti goma Khaleel ya shigo gidan ya kalli kujeran ya ga ta dauke kudin, ya haura sama xuwa dakinsa, yyi kwanciyarsa. Karfe daya Ashnaah ta idar da sllh Azahar har lkcn tana xaune kan darduman ta, ta kasa manta abinda ya faru daxu a kitchen, ko wani motsi tayi sae ta tuno scene din, hkn yasa ta kasa samun rest of mynd, ga wani yunwa da take ji kuma ta kasa sauka ta nemi abinda xata ci, mikewa tayi da kyar ta dauki electric kettle dinta ta nufi bathroom ta cire socket din washin machine ta sa na kettle din snn ta kunna ta fito, ko ba komae sae ta sha tean ta me kauri, sae da ta dauraye cup din snn ta ta Debi ruwan zafin ta dawo daki ta dauko kayan tean da har sun wuce rabi, sugar kam dama bae fi cube goma ya rage ba, ko kwakwaran kwana hudu kayan tean basu yi a dakinta ba, ta hada tean ta shanye snn tayi kwanciyarta nn da nn bacci ya dauke ta. Bude kofar ta da aka yi ya sanya ta farka a dan tsorace ta mike xaune da sauri tana kallon kofar, Khaleel ya shigo fuskarsa a daure yana mata mugun kallo yace "wa kika kira min da waya ta?" Ta dan xaro ido kmr munafuka ta ki cewa komae, ya daka mata tsawa "ba mgna nake maki ba", ta sunkuyar da kai don ko hada ido bata son yi da shi ynxu, murya can kasa tace "momyna na kira" tsawa ya kuma daka mata yace "dis shud be ur 1st nd last tym, at d first place ma me ya kai ki dakina" Ashnaah dae bata ce komae ba, ya tsaya yana mata mugun kallo can yyi kwafa ya karaso cikin dakin ya jefa wayar kan gadonta ya juya ya fice, ta bi sa da harara snn tayi tsaki can ciki, daukar wayar tayi ta Duba ta ga 5 min ago mum dinta ta kira kuma ya daga, dialing nmbrta tayi da sauri, bugu biyu aka daga cike da doki tace "momyna" mum dinta ta amsa daga daya bangaren tace "Na'am fateema ya kike" Ashnaah kmr xata yi kuka tace "lfya lau momy, ya gida" mum tace "lfya lau" Ashnaah ta dan yi jim snn tace"Abbana fa" momy tace "yana Abj" a hankali Ashnaah tace "momy in na xo baxae Kore bi ba" muryarta na rawa ta karashe mgnr, momy tace "ki bari sae in yana Abuja sae ki xo fateema," Ashnaah ta dan yi shiru nn da nn hawaye ya cika idonta a hankali tace "to momy me yasa Ashfah bata xo ba" Momy tace "kiyi hkuri Abbanku ne ya hanata xuwa, amma xata xo watarana, fatan dae kuna lfy bbu matsala ko" Ashnaah ta shiga share hawayen da ke xubo mata tace "ehh momy amma ni ban san shi ba wllh" momy tayi shiru snn a hankali tace"kiyi hkuri Allah xae maki sakayya" kasa cewa komae Ashnaah tayi, hkn yasa momy tace "to sae wani lkcn knn" Ashnaah ta gyada mata kai kmr tana ganinta hawaye na bin kuncinta a hankali tace "to ki gaida Inna" katse kiran tayi ta ajiye wayar ta shiga rusa kukan takaici, ta kai kusan minti talatin tana kuka Khaleel ya shigo dakin, kallo daya yyi mata ya dauke kansa ya karasa kan gadon ya dauki wayarsa ya fice daga dakin. Da la'asar tana xaune kan darduma ya bude dakin ta ya tsaya daga bakin kofar yace "in kin ga dama ki shirya xa ki je gaida kanwar Abbana" daga kai tayi tana kallonsa, shi kam tuni ya bar wajen, tayi tsaki tace "ba sae ka xo ka ja ni ba" gudun kar ya kuma dawo wa dakin ta shiga uku ne yasa ta mike a hankali ta fiddo kayanta ta, sae da ta fara shiga bathroom tayi wanka snn ta fito ta shirya, Karfe biyar ya kuma bude dakinta yana sanye da shadda sky blue colour, yana mata mugun kallo yace "amma baki san ke nake jira ba ko" ta mike ta dauki hijab dinta ta bi bayansa, bayan mota ta bude ta shiga abunta, ya juya xae mata mgna Suna hada ido ya kasa cewa komai yyi saurin dauke kansa ya bude driver seat ya shiga yyi warming motar suka bar gidan. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 34..... Biyar da kusan rabi Khaleel yyi parking a compound din su Meenah ya fito yana kallon agogon hannunsa ya nufi cikin gidan, Ashnaah tayi tsaki ta bude motar ta fito ta kulle snn ta bi bayan sa, bbu kowa falon ya haura sama, ita kuma ta samu kujera ta xauna, tana karema falon kallo, ko ina tsaf sae kamshi ke tashi, ba a dau lkci ba Anty fiddausi smll mum dinsa ta sauko dauke da murmushi a fuskarta ta karaso cikin falon tana ma Ashnaah sannu da xuwa, Ashnaah ta dan sunkuyar da kanta ta sauka kasa da ladabi ta gaisheta, hkn ba karamin mamaki ya ba anty ba, ta amsa da fara'arta tana tambayarta ya gidan, Meenah ce ta sauko kasa Momynta tace ta dauko ma Ashnaah drinks ta nufi kitchen sae ga ta ta dawo da faranti ta dire gaban Ashnaah tayi gaba abunta, Ashnaah ta bi ta da harara, Khaleel ne ya sauko daga sama ya xauna gefen smll mum din tasa yace "sannu Momy na" ta hararesa tace "me kke min a sama" yyi murmushin da ya bayyana dimples dinsa da fararen hakoransa yace "nothin mum kallo na tsaya yi a bedroom din ki" Satan kallonsa kawae Ashnaah take, ya daga kai ya kalleta ta dauke kanta da sauri tayi kmr kallo take, ya Mike ya nufi fridge ya bude ya dauko ruwa ya dawo falon ya xauna, hira suke tayi da mum din tasa ita dae Ashnaah mayar da hnklinta tayi kan program din da ake a TV, momy tace "xa ku jirani Khaleel xan dan fita in dawo ynxu" yace "its almost magrib fa mum ina xa ki" tace "eh nasani ba dde wa xan yi ba, gidan Hafsa xan tafi" yace "OK xa mu jira ki, ki gaida min ita don Allah in kin je" ta hararesa tace "wato ita ce ka raina baxa ka gidan ta ba ko kana ganin kan ku daya" Khaleel yyi dariya yace "not so wllh mum, xan je in Allah ya yrda" sama ta nufa ta dauko makullin motarta da mayafi tace ma Ashnaah sae ta dawo ba dde wa xata yi ba snn ta fita don xuwa gidan kanwarta. Khaleel ya Ciro wayarsa yyi dialing nmbr Zeenat yace "mu hadu garden mu yi mgna Zeenat" katse kiran yyi ya mike ya fita daga falon Ashnaah ta bi sa da kallo snn ta ja dogon tsaki ta tabe baki, Zeenat ta sauko sanye da wani material dinta me kyau ja da milk colour ta yafa mayafi milk colour, tun xuwan su gidan bata sakko ba sae lkcn, ta dan yi murmushi tana kallon Ashnaah tace "Sannun ku da xuwa" Ashnaah ta galla mata harara tace "ke dae xan ma sannu da xuwa, gun ki na xo xa ki wani ce min sannu da xuwa" Zeenat bata ce komae ba ta nufi kofa a sanyaye ta fita, bayan kmr minti goma da fitan ta sae ga Meenah ta sauko ta nufi kitchen da sauri, Ashnaah ta bi ta da kallo snn tayi tsaki, duk ta tsane su gaba daya, abinda ta ji Khaleel ya ce a waya ya dawo mata da sauri, wae sauko muyi mgna, to wacce mgnan xa su yi, da sauri ta mike a xuciyarta tace "Ae sae na ji wllh wllh" ta nufi kofa da sauri ta bude ta dan leka tsakar gidan ta ga ba kowa, hkn yasa ta fito a hankali ta durkushe a balconyn da sauri don kar a ganta ta shiga tunanin ta inda xata gansu a gidan, a dudduke ta fito daga balconyn ta nufi inda take tunanin kila xata gansu duk da bata san kan gidan ba, tafiya take kmr munafuka tana duddukawa, duk inda taga alamar hanya ne saka kafarta kawae take, tayi mmkin girman gidan kmr gidan su Khaleel, can ta hangosu xaune tsakiyar flowers kmr xae shige jikinta, ta sauke ajiyar xuciya, alhmdllh har ta shigo garden din knn ta fadi a xuciyarta, Ta duka ssae don kar su ganta ta shiga bin bayan flowers din da ya kewaye garden din har ta iso bayan wata flower inda ta tabbatar xata dinga jin abinda suke cewa ssae, ta duka da sauri ta ji sun yi karo da abu kmr mutum ssae ta tsorata har ta wage baki xata saka ihu ta ga Meenah ce, Meenah ta rufe bakin ta da sauri ita ma a tsorace alamar Ashnaahn tayi shiru, shiru Ashnaah tayi tana kallonta, sae kuma ta juya tana kallonsu Khaleel, yana xaune dab da ita yana facing dinta kan kujera, ita kam sae wani sunkuyar da kai take, Ashnaah ta ji Khaleel yace "kin yi shiru Zeenat" sae ga hawaye a fuskarta a hankali tace "ya Khaleel ni bna son komawa gida ynxu, nasan ina komawa Abbana ba tausayina xae ji ba dole sae ya hadani da Umar I knw" Khaleel yyi shiru yana kallonta snn yace "ba xae yi hka ba Zeenat xae ji tsoron a sake rasa ki, wata daya Ae ba wasa bace duk sun yi nadama na tabbatar maki, ni ynxu mum din ki kawae nake ji ma kince tana da hawan jini" Da sauri Zeenat tace "xan iya kiranta ko ynxu ne in mata bayanin komae I knw she wil b very happy hearin frm me after a long tym" Khaleel ya dan yi murmushi yana shafa sajensa yace "kar ki kirata tukun, ynxu dae ki ban digit din dad dinki I knw wat 2 do" tayi shiru tana kallonsa a dan tsorace, wani Sabon hawaye ne ya shiga bin kuncinta ya dago kanta da sauri yace "wae kukan me kike Zeenat" sunkuyar da kanta tayi da sauri, a hankali tace "bana son rabuwa da kai ya Khaleel" shiru yyi yana kallonta, ya dago kanta yana murmushi ya rungumota jikinsa yace "kar ki damu Zeenat we re still togeda bbu abinda xae raba mu" shiru tayi bata ce komae ba ya shiga share mata hawayen fuskarta da mayafin jikinta snn yace "to ban digit din dad" Ashnaah da ke ta wani xufa kmr me jin xafi ta juya tana kallon Meenah dake ta tabe baki tana kallonsu, a hankali tace"kin fito da wayar ki don Allah" murya can kasa Meenah tace "me xa kiyi da shi" Ashnaah tace "plss ki ban" Meenah ta bude pattern din wayar ta snn ta mika ma Ashnaah, dae dae lkcn da Zeenat ta shiga kira ma Khaleel nmbr dad dinta yana sa wa a wayarsa, Ashnaah ma ta shiga kwashewa da sauri da sauri, har Zeenat ta gama snn tana kallon Khaleel a hankali tace "watch ur wordz dear, kar kuma ka nuna masa kai ka daukeni don abun baxae mana kyau ba" Ashnaah ta mike da sauri ta na kallon Meenah tace "tashi mu je" Meenah ta jawo murya kasa kasa tace "ki jira su tashi mana sae mu bi ta kitchen" ba musu Ashnaah ta koma ta xaune kan carpet grass din, Khaleel ya mike yana kallon Zeenat yace "tashi mu shiga kafin mum ta dawo its almost magrib" Zeenat ta mike ya kama hannunta suka nufi cikin gida ta front yrd, mikewa Meenah tayi da sauri tace "kin dae iya gudu ko" Ashnaah ta Mike tace "eh" snn suka nufi cikin gida ta kofar kitchen da gudu kar su Riga su shiga, sama suka nufa da gudu Meenah ta bude dakinta suka shige suna mayar da numfashi. [10/10, 6:43 AM] ‪+234 701 117 6189‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 35..... Khaleel na shigowa falon yyi mamakin rashin ganin Ashnaah, ya juya yana kallon Zeenat da ke bayansa yace "ina yarinyar nn take" Zeenat ma ta shiga bin falon da kallo tace "xaune naganta daxu kafin in fita ban san inda tayi ba kuma" juyawa da sauri yyi ya fice daga falon xuwa gun mai gadi, "don Allah baba kaga wata ta fita daxu" mai gadin yyi shiru snn yana girgixa kai yace "gskya bbu Wanda ya fita tun bayan fitan hajiya" wani ajiyar xuciya Khaleel ya sauke ba tare da ya sani ba, ya juya ya kuma komawa cikin gidan, har lkcn Zeenat na tsaye gun da ya bar ta, sama ya nufa ya bude dakin Meenah, Meenah na xaune kasan dakin sae faman hira take ma Ashnaah dake xaune kan gadonta tana kyalkyala dariya, tsayawa kallonsu yyi da mamaki, Ashnaah ta dan yi tsaki tace "dalla ci gaba Meenah" Meenah ta Mike daga xaunen da take a kasa ita ma tayi tsakin tace "ni tsoro ma aka ban wllh, mutum in xae shigo dakin mutane ba sae yyi sallama ba" karaso wa cikin dakin Khaleel yyi, Meenah ta nufi bathroom dinta da sauri ta shige ta rufe, Khaleel na ma Ashnaah wani mugun kallo yace "me kike yi a nn" xaro ido tayi tana kallonsa tace "ban gane me nake yi ba, don me ka kawo ni nn, ba don in yi xumunci ba, don kuma ina hira da yar uwarka shine nayi laifi" ta tabe baki ta dauke kanta, kallonta kawae ya tsaya yi, can yace "tashi ki fita" bae rufe baki ba ta galla masa harara tace "sllh xan yi" a fusace ya karaso inda take ya fixgota ta mike a tsorace ta rike hannunsa tace "don Allah kayi hkuri wllh xan fita dama sllh na shigo yi" bata jira me xae ce ba ta fice daga dakin da sauri, dole a bayin kasa tayi alwala yace Zeenat ta dauko mata sallaya tayi sllhn a falo, Zeenat ta sauko rike da darduman ta mika ma Khaleel snn ta koma sama, Ashnaah ta tabe baki tace "ni dae bn aiketa ba, kuma in har ita ke sllh kae to baxan yi ba" Khaleel yace "kin fi ta tsafta ne" mikewa Ashnaah tayi a fusace tace "wnn ce ta fi ni tsafta, Ae da na ji haushi wllh, ko kai ka gwada min tsafta bare wnn bnxar" mikewa yyi yana nunata da yatsa yace "watch ur tongue" ta dauke kanta ta ja tsaki, ya nufi sama don yin alwala ya tafi masallaci. Ashnaah na idar da sllh momy ta shigo, Ashnaah ta yi mata sannu da xuwa ta amsa tace "ke kadae kuma a falo fateema me yasa baki hau sama ba, ina su Aminan suke" Ashnaah tayi murmushi bata ce komae ba, momy ta nufi kitchen, sae ga ta ta fito rike da abinci da drinks a faranti ta kawo ta ajiye gaban Ashnaah tace "ga abinci fateema" Ashnaah tace "ngd momy" takwas saura Khaleel ya shigo gidan, Ashnaah na xaune da momy da Zeenat a falo, momy tace Zeenat ta kawo masa abincin sa kan dining, yace "wllh mum ni kam a koshe nake," Momy tace "me kaci xaka ce ka koshi?" Ashnaah tace "dama hka xae ce momy, sae mun koma gida yace sae na masa girki" da sauri Khaleel ya juya yana kallonta, ta galla masa harara, momy tace "to ku tafi da shi mana, amma da Daren nn wani girki xa a yi in an koma gida" Khaleel yyi murmushi yace "to momy xan tafi da shi" mikewa Khaleel yyi yace "momy dare na yi bari mu kama hanya" momy ta Mike tace "to bari in sa maku kulan a leda" dinnin ta nufa sae ga ta ta dawo da abincin ta mika ma Khaleel, yyi mata gdya Ashnaah ta mike tace "bari mu yi sallama da Meenah" sama ta nufa Khaleel ya bi ta da kallo ba daman ya bi ta, ta samu Meenah ta fito daga wanka tace "ke xa mu tafi, dan yi min copyn din nmbr nn a paper" Meenah tace "to har ynxu ba ki gaya min me xa ki yi ba Ae" Ashnaah tace "ke dae ki rubuta min, yaushe xa ki xo" Meenah tace "aa ni tsoron mijin nn naki nake" Ashnaah tace "dalla can ki xo, me ya isa yyi maki ina nn, Ae baxan bari ba" Meenah tace "to gobe idan Allah ya yrda xan xo" Ashnaah tayi murmushi tace "ko ke fa" nmbrs din Meenah ta kwafe mata a takarda ta mika mata, Ashnaah ta karba ta ce "yawwa kawas sae kin xo" snn ta fice da sauri. Har suka bar gidan Khaleel bae daina Satan kallon Ashnaah ba, sae da suka bar anguwar snn yyi parking yana kallonta fuskarsa a hade yace "me kika je yi a sama" Ashnaah ta ce "sallama fa naje muka yi" yana kallonta da kyau yace "kina ji na" ta yi shiru tana kallonsa, ya ci gaba "bbu ke bbu yarinyar nn, kika bari na sake ganin ku tare sae na..." Da sauri tana hararansa tace "A'ah, sbda me ba yar uwarka bace" fixgota yyi yace "ni kike tambaya sbda me" da sauri tace "aa kayi hkuri na ji wllh" yyi kwafa ya turata, yace "meye kike boyewa cikin hijab" ta Ciro turaren da momy ta bata da sauri ta nuna masa, dauke kansa yyi ya ci gaba da tukinsa. Karfe tara saura Khaleel yyi parking a gidan sa, ya fito yana jiran Ashnaah ta fito, ta fito snn ya kulle motarsa ya nufi cikin gida, ta dan yi tsaki ta shiga bin sa a baya, falo ta same sa a xaune ya kunna TV, yana bude abincin da smll mum dinsa ta basa, Ashnaah ta tsaya daga bayan kujerar da yake xaune ya juya da sauri yana hararanta yace "meye kika wani tsaya a kaina" ta koma baya tace "aa dama cewa xan yi in kawo plate ka debar min don ina jin kunya ban ci da yawa a can ba kuma ynxu yunwa nake ji" tsayawa kallonta kawae Khaleel yyi, can ya girgixa kai yace "kika bari na tashi wllh sae kin sha mamaki, ta shi min a bayana" ya karasa mgnr cikin tsawa, ta koma baya da sauri don ta ji tsoron tsawan da yyi mata, can tayi tsaki ta nufi sama kmr xata tashi sama. 36..... Karfe sha daya da kusan rabi Ashnaah na kwance dakinta bayan ta gama shan tea, kmr warce ta tuna abu ta mike xaune da sauri ta nufi gaban madubinta ta dauki takardan da Meenah ta rubuta mata nmbr dad din Zeenat tana kallo, to ynxu ita ina xata samu wayar da xata kira nmbr nn, ta koma gefen gadonta ta xauna tayi tagumi tana tunane tunane, duk fa na ynda xata samo waya, bude kofar dakinta aka yi ta boye takardan da sauri a bayanta tana kallon kofar, Khaleel ya shigo dakin rike da kulan abincin yana kallonta yace "mayya! kin sa na kware hankalinki ya kwanta, sae ki cinye abincin" yyi tsaki ya fice daga dakin, Ashnaah ta tabe baki tace "ni ba mayya bace sae dae in kai ne mayye" ta mike ta dauko abincin ta bude taga kadan ya ci, naman kam bata ga alaman ya taba ba ma, tayi murmushi ta dauki spoon din ta shiga cin kayanta, tana gamawa ta shiga wanka, ko da ta fito hijab kawae ta xura bayan ta goge jikinta ta dauki kulan da ta ci abinci ta fita don xuwa ta kai shi kitchen. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 37..... Ashnaah ta tabe baki ganin duk ya kashe wutan gidan sae dim blue light da ya bari a kunne a falon, kitchen ta nufa ta kunna wuta ta ajiye abin hannunta a sink snn ta kashe wutan ta fito ta kulle kitchen din ta nufi sama, har ta bude dakinta xa ta shiga sae kuma ta juya tana kallon kofar Khaleel, to ko dae ta sato wayarsa ynxu ne tayi abinda xata yi don bata son ya riga ta kiran dad din Zeenat, a hankali ta nufi kofar falonsa, ta kusa minti biyar tana tunanin ta shiga ko kar ta shiga, daga karshe ta murda kofar a hankali ta leka falon ta ga a kashe wutan falon yake, hkn yasa ta shiga ta karasa xuwa bedroom dinsa cikin sanda, ta ji kofar ma a rufe, gabanta ya shiga faduwa, to in idonsa biyu ya xata yi knn, tunanin hkn yasa ta kuma tsorata ta juya da gudu ta koma can bakin kofar falon xuciyarta na bugawa, kamshin sabulu da ta dinga ji ya gauraye duk falon yasa tace to ko dae wanka yake, komawa kofar dakin tayi ta kasa kunne bakin kofar taji kmr saukan ruwa a bayi, hkn yasa ta murda kofar a hankali inda Allah ya taimake ta ma kofar ko kadan baya kara, ta leka dakin taga dim bedside lamp ne kadae a kunne, ta shiga dakin ta nufi gaban madubi da sauri ta laluba bata ga wayar ba, dudduba gado ta shiga yi tana laluba ko ina ko xata gani amma bata ga alamar waya ba, ba karamin haushi hkn ya bata ba har ta fidda rae xata fita ta hango wayar can kan bedside drawer ta daya bangaren da take tsaye, da sauri da sauri ta nufi gun, ta duka ta dauki wayar, ta juya xata bar wajen knn taji an bude kofar bathroom, ji tayi kmr an buga mata guduma a kirji tsabar faduwar gaba, ta tsaya cak har lkcn wayar na hannunta sae rawa jikinta yake, da mugun mamaki Khaleel ke kallonta, ta dake taki kallon inda yake, ta ajiye wayar hannunta ta juya da sauri xata bar wajen yyi saurin fixgota ta fado kirjinsa, dama kuma dae dae nn take kai sa, ta dago kai a tsorace tana kallonsa, ssae taji tsoron ynda ta gansa ta rufe idonta da sauri ta mayar kan faffadan kirjin nasa ta saki kuka tana cewa "wayyo ni fa agogo na xo dubawa na daki na ya tsaya" Like · 2 · Reply · Report · ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 38..... Khaleel ya dago kanta yana wani irin murmushi yana kallon fuskarta, runtse idonta tayi ta ki Budewa tana kuka a tsorace tana cewa "Don Allah don annabi kayi hkuri agogo na xo dubawa ne" ji tayi ya dauketa cak, ta bude ido a tsorace ta gansu kan gado, wani Sabon kukan ta fashe da tana kkrin mikewa da sauri ya matse ta jikinsa, cikin tashin hnkli ta shiga cewa "wayyo don Allah kayi hkuri baxan sake ba wllh" wani irin kallo yake mata da idonsa da ya canxa launi, ta shiga turasa a rude tana kuka tana nasa hkuri, bata ankara ba taji ya saka bakin sa cikin nata ya shiga mata wani mugun kiss lkci daya yana kkrin cire mata hijabin jikinta, tunda take bata tsorata ynda tayi ba a lkcn barin ynda ta gansa kmr ba shi ba, fixge fixge ta shiga yi amma ta kasa kwace kanta, bbu abinda yafi daga mata hankali irin ynda tasan xani kadae ne jikinta, tsaf ya cire hijab din jikinta, Ta rike xaninta gam ganin yana neman cire mata shima, jikinta na rawa cikin kuka ta shiga cewa "wayyo na shiga uku don Allah kayi hkuri wllh xani kadae ne jikina plsss kayi hkuri" rungumeta yyi gam yana mayar da numfashi, bbu abinda take ji sae bugun xuciyarsa da saukan numfashinsa a wuyanta, ita dae tana rike da xanin ta gam jikinta na rawa har lkcn, turata taga yyi ya mike da sauri ya nufi bathroom, bata tsaya wani tunanin ba ta mike da gudu ta fice daga dakin ba tare da ta bi ta kan hijabinta ba, ta shige dakinta ta kulle da key ta xube nn kasa ta dinga rusa kuka jikinta na rawa har lkcn, ta ci kukanta me isarta snn ta Mike xaune har lkcn xuciyarta bae bar bugawa ba, ynxu da abu ya shiga tsakaninsu ya xata yi, tab da ya cuceta ya lalata mata rayuwa kuwa, tunanin hkn yasa wani mugun tsanarsa ya dirar mata a xuciya, ta mike a hankali ta nufi kan gadonta ta xauna, ae da ta ba wnn axxalumin kanta gwara Allah ya dauki ranta, tsakin takaici ta ja, ta Mike ta bude wardrobe dinta ta dauki dogon rigar baccinta ta sa, snn tayi kwanciyar ta ta ja bargo nn da nn bacci ya dauketa. washegari da safe tana wanka taji fitar motarsa, ta ja tsaki ta gama wankanta ta wanke bathroom dinta snn ta fito ta gyara jikinta ta sa doguwar rigar da ta fito da ta sauka kasa don neman abun kari, a rufe ta tadda kitchen din, ta bude baki tana kallon kofar da mmki, ji tayi kmr ta balle kofar, ta ja dogon tsaki tace "banxa kawae axxalumi" a fusace ta koma sama ta xauna kan gadonta, sae kuma ta fashe da kuka tana kiran momynta, ta kusa minti goma tana kuka, kawae ta tuna kudin da Al ameen ya bata, ta mike da sauri ta bude Jakarta ta dauko, murmushi tayi ta cire dubu daya a ciki snn ta mayar da sauran ta sauka kasa abunta ta nufi gun masu gadi, gaisheta yyi da ladabi tace "lfya lau dama Aiken ka xanyi" yace "to madam me xa a siyo maki" tace "eatry xa ka je ka siyo min abinci ko ma wani iri ne" yace "to madam amma sae David ya dawo ya tsaya bakin gate tunda mai wanki baya nn," Ashnaah tace "to barayi ne a anguwar da baxa ka je ka dawo ba ynxu" yace "aa ba hka ba madam, oga baya son ana barin gate hka nn sbda ke wae" tsaki tayi ta juya ta bar wajen tana cewa sbda gidan sa dae ba ni ba, tana kwance falo tana kallo aka danna bell ta Mike da sauri don tasan abincin aka kawo mata, tana karba ta kulle falon ta dawo ta bude taga jollof ce da nama, sama ta nufa ta wanke hannunta snn ta sauka ta shiga cin abincin ta, tana gamawa ta koma sama ta shiga bayinta ta sha ruwan tap snn ta fito ta kwanta sae bacci. cikin bacci taji ana danna bell din gidan, ta sauko da sauri gabanta na faduwa, ta dan leka kofar taga fuskar Ummi, wani kara ta saki ta bude kofar da sauri ta rungumeta ba tare da ta lura da sauran kawayen nata ba, Aisha tace "wato ummi kadae kika sani ko" juyawa tayi da sauri tana kallonsu ta wara ido cike da jin ddi tace "waw amma kun burgeni wllh don Allah ku shigo, kai naji ddi ganin ku wllh" rasa abinda xata basu Ashnaah tayi, ta nufi sama da sauri ta Ciro dubu daya cikin kudinta ta sauko tace masu tana xuwa ta nufi gun mai gadi, ta basa kudin tace soft drinks da ruwa ba duka xae karbo mata, ya karbi kudin snn ta juya ta koma cikin gidan, "amma wa yyi maku kwatance ku ka gane hka" Ummi tacev"Anty shafa mana, wae Ashnaah ya maganar karatun ki, baxa ki lallaba mijin ki ba ya bari ki koma, Kinga next month xa mu fara exams fa" Ashnaah ta marairaice ta xauna tana kallonsu tace "Ku ce Allah next month be exams" bilkisu tayi dariya tace "Sae ma mun ce Allah ko" Ashnaah kmr xata yi kuka tace "to wa xae bar ni in koma ynxu..." sae ta fashe masu da kuka abun dariya abun tausayi, ummi ta danne dariyarta tace "to meye abun kuka, baxa ki lallaba mijin ki ba ya bari ki koma" nn da nn Ashnaah ta daina kukan ta hade rae tace "waye mijina kuma" Ummi da sauran suka kwashe da dariya suka ce "mai gidan nn mana" Ashnaah ta hade rae tace "kun ga in kun san xarafi na ku ka xo ci to ku tashi kuyi tafiyar ku ngdd" ssae suka dinga dariya Ashnaah da ta kulu matuka ta rasa ma me xata ce masu, Khadija tace "kinga ynxu dae ayi facing reality, wllh ki lallabasa ya bari ki ci gaba da karatun ki kar ki cuce kanki" Ashnaah tace "in lallaba wa? tabdi" tsaki tayi dae dae lkcn da aka bude kofar falon, Ashnaah ta mike da sauri kuma a tsorace don ganin Wanda xae shigo, Khaleel ne ya shigo falon yana sanye da farar 3qtr da bakar polo yana rike da leda a hannunsa, hanjin cikin Ashnaah sae da ya kada dob tsoro amma ta wani hade rae duk da irin ynda gabanta ke faduwa ta koma ta xauna,cikin tafiyarsa ta kasaita ya karaso cikin falon yana kallon frnds din nata, Ummi ce kadae tayi karfin halin gaishesa, ya amsa murmushi dauke a fuskarsa snn sauran ma suka gaishesa ya amsa duk yana tambayarsu ya hanya, suka amsa da lfya lau snn ya ajiye ledan hannunsa nn gaban Ashnaah ya nufi sama, Aisha tace "wae wnn shine mijin naki Ashnaah" Ashnaah ta tabe baki tace "gashi kin gane ma idon ki kuwa" Bilkisu tace "waow amma ya hadu ya hadu har ya gaji kai!" hade rae Ashnaah tayi amma bata ce komai ba sae tabe baki da tayi, Aisha tace "tabdi, wnn din ne baki so Ashnaah, wayyo ina ma ni na samesa" Ashnaah ta kuma hade rae bata dae ce komai ba, Ummi kam hmmm kawae tace, Maryam tace "to baxa ki tafi ki masa sannu da xuwa ba" a fusace Ashnaah tace "Don Allah ku rabu dani" ummi ta mike tace "kun ga muna da lecture Karfe daya ku tashi mu kama hanyar sch, gashi ma mijinta ya dawo mu kama gabanmu" Ashnaah tace "haba plss da wuri hka dama ba yini Min kuka xo ba" kmr xata yi kuka ta karashe maganar, Ummi tace "kar ki damu xa mu dawo fateema, muna da test ne Yau wllh" Ashnaah ta bude ledan da Khaleel ya ajiye mata taga take away na abinci ne da drinks, tace "to ga abinci ku tsaya ku ci plss" duk suka ce a koshe suke, ta bata rae tace "au hka xa ku min" dariya suka yi suka ce kar ta damu sae sun kuma dawowa, suna tsaye bakin kofa Khaleel ya sauko shima xae fita, Ashnaah ta juya tana kallonsa tace "wae xa su tafi fa" rasa ma me xae ce mata yyi, can yace "OK ina xuwa" snn ya koma sama, ummi tace "kai Ashnaah to me xae mana" saukowa yyi yana rike da car key yace "mu je in sauke ku to" da sauri Ashnaah tace "A'a kudin mota fa xa ka basu kasan inda xa su ne" ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 39..... Dubu biyar Khaleel ya ciro ya mika mata yana kallonta, ta karbe kudin ta bi bayan frnds dinta da sauri don har sun bar falon suna dariya, bin ta yyi da kallo ganin ynda take tafiya har ta isa gun frnds din nata snn ya kauda kai, da kyar Ashnaah ta tilasta su suka karba kudin don kin karba suka yi da wae sun gode, Khaleel dae na tsaye daga bakin kofa yana danna wayarsa lkci lkci ya kan daga kai ya kallesu, ummi tace "to ki taya mu yi masa gdya Ashnaah, sae wani lkcn kuma" da sauri Khaleel ya daga kai yana kallon Ashnaah jin sunan da ummi ta kirata da shi wae Ashnaah, meye kuma Ashnaah, Ashnaah kam har bakin gate ta rakasu snn ta dawo abunta, har lkcn yana tsaye daga bakin kofa, ta gefensa ta bi xata shiga falon ya fixgota yana mata wani irin kallo yace "wa ya baki izinin shigo min da baki gidana?" Duk da ta dan tsorata amma hkn bae Hana ta dakewa ba tace "to ni nasan ma wa ya kawo su ba kawae ganinsu nayi ba nima" kallon cikin idonta yake, ita ma hka, sunkuyar da kanta tayi da sauri don hka kawae taji kunya ya kamata tuna abinda ya faru jiya da daddare da tayi, ko hkn ya tuna shima oho, don kawae gani tayi ya dauke kai shima ya saketa ya nufi gun dayan motarsa da ke Parke a parkn space din gidan, don Wanda ya saba fita da ya baro shi a clinic, Ashnaah ta shige falon da sauri abunta, sae da ta ji fitar motarsa snn ta bude abincin da ya kawo mata, tuwo ta gani da miyar vegetable yaji nama da kaza, nn da nn ta mike da sauri ta hau sama ta wanke hannunta ta sauko ta shiga tura kayanta, bude kofar falon aka yi ta juya da sauri har xata boye abincin ta ga Meenah ce, ta Mike da sauri tana washe fararen hakoranta tace "lah ashe dae xa ki xo, shigo mana kika tsaya daga bakin kofa" Meenah tace "amma dae Khaleel baya nn koh" Ashnaah tace "waye kuma Khaleel" tsakaninta da Allah tayi tambayar don manta sunansa take, Meenah ta harareta, da sauri tace "ohh ya fita ynxun nn, kinsan ni manta sunansa ma nake wllh wllh" Meenah ta karaso falon har lkcn tana hararan Ashnaah tace "sunan mijin naki kike mancewa" Ashnaah tace "wllh mance sunansa nake, khaleed ko wa yake, to wae ma ba sae ka damu da mutun xaka rike sunansa ba" Meenah ta fashe da dariya tace "ban gane ba, ke da sweetyn naki kuma" Ashnaah ta tabe baki tace "sweetyn su dae, Sweetyna na inda yake, Allah sarki usman" Meenah da mmki tace "ban gane ba" Ashnaah tace "ae idan da Akwae Wanda na tsana a duniya a ynxu bae wuce dan uwanki ba, Allah yasa baxa ki ji haushi na ba" Meenah ta xaune nn gabanta tace "ke bani in sha, ae nima duk duniya bn jin Akwae wnda na tsana irinsa, amma ina kuka hadu da shi to har kika yrda kika auresa, ae da na ganki kafin lkcn bikin da na baki shawaran kar ki auresa don...." Ashnaah ta fashe da kukan takaici ta shiga ba ma Meenah lbrin ynda Khaleel ya aureta, har ta gama lbrin bakin Meenah a bude yake, don kanta daga Karshe ta rufe bakin tace "ikon Allah, sae kace a film, amma shine kike xaune har Yau a gidan sa baki san ynda kika yi kika fidda kanki ba" Meenah ta girgixa Kai da mugun mamaki tace "kan bu, amma naga kkrin ki ae in nice wllh wllh bna kwararren sati biyu a gidan ka, ka hada ni da abbana ka raba ni da momyna, kayi sanadin daina karatuna uban me xan yi gidan ka, kai har kin bn haushi wllh, wayyo ina ma ni ce" Ashnaah ta dan marairaice tace "to bn san ya xan yi ba Meenah, bbu irin fitsarar da bana masa amma sae dae ma ya nakada min shegen duka" Meenah ta xaro ido tace "duka? Kika tsaya yake dukan ki, amma ke bnxa ce wllh" Ashnaah tace "to ae ba iya ramawa xan yi ba baki ganin ynda yake ne, Kinga wani lkcn ma da yunwa yake bari na fa wllh, ynxu ki tafi kitchen ki ga a kulle yake tun safe yar shinkafa na bada kudin a siyo min" ta karashe mgnr kmr xata yi kuka, a hnkli Meenah tace "amma dae tsaya, baki basa kan ki ba dae koh" Ashnaah tace "sae kace ina hauka tabdi" Meenah tace "to alhmdllh, amma dae meye to na kishi da kika ji ya ce xae aure Zeenat har da wani daukan nmbr babanta" Ashnaah tace "kishi kuma, ae so nake in gaya ma Baban Zeenat din shine ya dauke masu yar su don su hukunta shi" Meenah ta fashe da dariya tace "kuma fa hka ne, to ynxu kin kirasa din ne, Ashnaah tace " ina naga wayar kiran, ae bani da waya, ki ara min naki ynxu in kira" Meenah ta xaro ido tace "baki san xa a iya ganowa ba, kuma gashi Zeenat din tasan nmbr na" Ashnaah tace "to ina da dubu takwas in baki ki siyo min waya karama sae a sa Min sim, ae kudin xae isa ko" Meenah tace "to mu tafi tare mana" Ashnaah ta xaro ido tace "ae ya gaya ma masu gadin kar su bar ni in fita, da ana bari na in fita da tuni na gudu na kara gaba ae" Meenah ta fashe da dariya, Ashnaah tace "bari in dauko kudin" meenat tace "to amma ba ynxu xae dawo ba dae ko, kar ya xo ya sameni in shiga uku" Ashnaah tayi dariya tace "ae sae dare yake dawowa gantalallen" ~Dr Khaleel ~ By Khaleesat Haiydar 40..... Ashnaah ta sauko rike da dubu takwas din da ya rage cikin kudin da aka bata ta mika ma Meenah, Meenah ta kirga snn ta xuge jaka ta xuba su ciki ta kulle, tana kallon abincin gaban Ashnaah tace "to ina kika samo tuwon nn" Ashnaah ta dan tabe baki tace "wae fa kansa ya siyo ma xae ci to da ya gan ni da baki sae kunya ta kamasa kmr xae nutse shine fa ya ajiye min, kinsan dae ba sata kadae bne abun kunya" dariya kawae Meenah ke yi, ita kam komae na Ashnaah dariya yake bata, gata dae yarinya amma in ta xaro maka mgna sae kace babba yyi ta, Ashnaah na kallonta da mamaki tace "ae gskya ne, ko ruwan fa da xan sha gidan nn bbu sae dae in je in sha na famfo duk tsutsa, ko me aikin gidan mu wllh ruwan gora take sha, to ina dalili" Meenah tayi dariyarta me isarta tace "to shi wani ruwa yake sha tunda bbu ruwa a gidan" Ashnaah tayi murmushi ta mike tace "ina xuwa in nuna maki" sama ta nufa ta bude falonsa ta shiga snn ta nufi fridge dinsa, a rufe ta tarda fridge din ta cije dan yatsa a xuciyarta tace "ae sae na nema wllh" bbu rabon xata wahala ta hango keyn kan fridge din ta bude da sauri tana kallon ciki, wines din basu fi biyar ciki ba, biyu iri daya, uku iri daya, kinkimansu tayi gaba daya ta nufi gun Meenah ta dire su gabanta ta nemi guri ta xauna tace "kin gansu nn" da mmki Meenah ke kallon kwalaban ta daga tana kallon Ashnaah tace "wnn ae giya ce fateema" Ashnaah ta tabe baki tace "to su ne ruwansa a gidan nn, in ya kafa kai baya ajiyewa sae ya kwankwade gaba daya" Meenah da kanta yyi mugun daurewa tace "dama Khaleel na shan giya" Ashnaah tace "gashi ko kin gani, suna can da yawa a fridge dinsa kala kala" Meenah tace "haba shi yasa ko da yaushe xan ji fridge dinsa a rufe idan naje can gidan su" Ashnaah tace "to ynxun ma an gaya maki a bude na samu, da kyar na samo makullin," Meenah tace "dole ko da yaushe xaka gansa cikin rashin fara'a, kin san Allah tunda nake kallon arxiki bae taba hada mu ba" Ashnaah tace "ga tuwo ki ci bari in je inyi sllh, ko azahar bn yi ba" Meenah tace "to je ki dawo in baki wata shawara" Ashnaah tace "to" snn ta nufi sama don yin alwala tayi sllh. Khaleel na xaune office bayan ya fito daga theatre ya jinginar da kansa jikin office chair dinsa idonsa lumshe kmr me bacci aka bude office dinsa, ya bude ido da sauri don ganin wanda xae shigo, Ameesha ce ta shigo office din da sallamarta, ya mayar da kansa ya lumshe idonsa, ta dan tsaya nesa da shi tace "ka gaji koh" ya bude ido yana kallonta yace "yep, bacci ma nake ji" tace "to abinci fa, ina tuwon da na kawo maka daxu" ta fadi hka tana dudduba abincin a office din, da kmr baxae ce komae ba sae kuma yace "sorry na bayar da shi" shiru tayi tana kallonsa, ya mike xaune da kyau yace "kin yi fushi ne" girgixa masa kai da sauri tayi, yyi murmushi yace "amma ae na ci kadan, vegetable din yyi ddi, kin yi kokari, u re a gud cook" murmushi tayi da ya kara fito da ainahin kyanta, a hankali tace "thank yhu" ya gyada mata kai yana murmushi snn yace "gida xa ki ynxu ne" ta gyada masa kai alamar eh, ya mike ya dauki makullin motarsa yace "mu je gidana ki min girki sae in kai ki gida" shiru tayi tana kallonsa, yace "ko baxa ki bne" a hnkli tace matarka fa, ya galla mata harara yace "waye hka" kasa cewa komae tayi sae kallonsa take, yyi tsaki ya kwashi wayoyinsa yana kallon agogo ya ga Karfe biyar saura, Yace "mu je in xa ki" ba musu ta bi bayansa suka fita ya kulle office dinsa, sae da ta fara xuwa office din dad dinta ta dauki handbag dinta snn ta sauko tayi ma sauran nurse din sallama ta nufi gun motar Khaleel don yana ciki yana jiranta. Ashnaah da Meenah na xaune har lkcn a falo, Ashnaah na digestin duk abinda Meenah tace mata, bbu irin abinda Meenah bata kintsa mata ba, gate suka ji an bude, Meenah ta mike tsaye da sauri tace "waye hka xae shigo" Ashnaah ta wara ido tana kallon agogo, jin karar motar Khaleel yasa ta kalli kwalaban wine din dake xube gabansu har lkcn bata mayar ba, mikewa tayi a tsorace tace "wayyo na shiga uku shine ya dawo, me ya dawo da shi ynxu" Meenah ta xaro ido ita ma a tsorace tace "kin shiga uku ko na shiga uku," kwashe kwalaben Ashnaah tayi ta nufi kitchen da su da gudu jikinta na rawa sae kuma ta fito da su duk a rude, sae ca take na shiga uku ina xan Kai su xae iya shiga kitchen ya gansu, kitchen ta kuma komawa da sauri ta boye su cikin store, ko da ta fito bata ga Meenah a falon ba, xata bar falon ita ma aka bude kofa, ta juya da sauri tana kallonsa nn da nn ta hade rae, ya kwaso takalman da ya gani bakin kofa da mamaki yana kallon Ashnaar yace "takalman waye wnn" ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 41 Shiru Ashnaah tayi tana kallon Ameesha da ke bayan Khaleel ta ki shigowa, ya daka mata tsawa yace "ba kya ji na ne, nace takalmin waye wnn" Ashnaah tace "wacece wnn a bayan ka" bude baki yyi da mmki yana kallonta yace "ina maki tambaya kina min tambaya" dauke kanta tayi fuskarta a daure taki cewa komae, ya kuma daka mata tsawa yace "nace takalmin waye wnn" ta juya tana kallonsa tace "sae ka fara gaya min wacece wancan a bayan ka" ta karashe mgnr tana hararansa, ihu ta fasa ganin ya yo kanta ta nufi bayan kujera da sauri tana cewa "wayyo wllh xan gaya maka ka tsaya" ganin kamata yake son yi yasa tace "don Allah kayi hkuri na wa ne ina son in fita in siyo abu ne sae mai gadi ya hanani, sae na manta ban shigo da shi ba" tsayawa kallonta yy, yyi kwafa yace "bace min a falo" hararan Ameesha tayi snn ta haura sama. Bayan kofarta ta tarda Meenah a labe, ta fada kan gado ta dinga kyalkyala dariya, Meenah ta fito da sauri ta mata alamar tayi shiru, Ashnaah tace "ae ba shigo wa xae yi ba," a hankali Meenah tace "to ya xa ayi in bar gidan nn yau, ga shi nace ma momy ba ddewa xan yi ba" Ashnaah tace "ae xae shi ga dakinsa sae ki fita da gudu, muyi hirar mu don Allah," Meenah ta galla mata harara tace "da wani bakin xan yi hira, kin san ynda ciki na ke kara kuwa, ba mutun ci gare mijin nn naki ba sae ya iya wurga ni waje wllh" Ashnaah tayi dariya tace "to sae kiyi ta tsayuwan, nace maki baya shigo min daki sae in nayi laifi" dakinsa suka ji ya bude, Meenah ta koma bayan kofa da sauri har tana bugewa, Ashnaah ta toshe bakinta kar ta Tona masu asiri da dariya, fitowa Meenah tayi tace "to ya shiga dakin, ta ina xan bi" Ashnaah ta mike tace "ina xuwa" snn ta fice, ba a jima ba ta dawo rike da takalman Meenah tace "oya xo ki gudu yarinyar da ya kawo ma na kitchen, amma yaushe xa ki kuma dawowa don Allah" Meenah tace "gskya ba ynxu ba" Ashnaah ta marairaice tace "haba don Allah to wayata fa gashi fa kinsan abinda yasa nake son siyan wayar" Meenah tace "to xan yi kokari gobe in na siya in kawo maki amma fa baxan dde ba" Ashnaah tace "yauwa don Allah kar ki manta ki siyo min maganin ciwon ciki in xaki xo, wllh tsoro nake ji period dina ya kusa xuwa kuma wahala nake sha wllh, ynxu ma ya fara damuna" Meenah tace "to Allah sa kar in manta" Ashnaah ta riko hannunta tace "Aa don Allah kar ki manta ki siyo min, ina jin jiki in ina yi" Meenah tace "to naji, amma kuma ba ga ki da likita a gida ba" Ashnaah ta bude baki tace "au likita ne, ki ce wllh" Meenah tayi dariya tace "ohh da baki sani ba, wllh likita ne kuma babba ma" Ashnaah ta tabe baki tace "oho ni ina na sani" Meenah ta saka takalminta tace "kin ga sae na xo" a hnkli ta bude kofar ta shiga sauka daga stairs da sauri, da gudu gudu sauri sauri kmr munafuka ta fice daga gidan gaba daya, Ashnaah da ke lekenta ta window sae dariya take har da kyakyatawa tana rike ciki, bude kofar ta taji an yi ta juya da sauri taga Khaleel ne, da mmki yace "ke kina da hnkli kuwa, wa kike ma dariya a window" Ashnaah ta kuma kwashewa da dariya har da durkushewa inda take tana rike ciki tana kallonsa, dariyar shima ta basa, ya kauda kansa yyi murmushi ya juya ya fice daga dakin, sae da ya sauka kasa snn shima ya shiga dariyan, anya yarinyar nn ita kadae take kuwa tambayar da yyi ma kansa knn bayan ya shigo falo. Har Ameesha ta gama girkin da Khaleel ya sa ta Ashnaah bata fito ba, tasan kila adduarta Allah ya amsa, don tun da ta shigo kitchen din take adduar Allah yasa kar Ashnaah ta sauko, don ita hka kawae take tsoron ta, kan dinnin ta jera masa abincin ta karaso falon tana kallonsa tace "na gama," ya mike xaune yana kallonta yace "thnk yhu dear, kawo nn mu ci" ta girgixa masa kai tace "ni na koshi gida xan tafi" ya harareta yace "ae kya bari in ci abinci ko" murmushi tayi ta gyada masa kai, yace "to kawo min abincin nn falo" juyawa tayi ta je ta dauko abincin ta shigo falon ta ajiye masa gabansa, bin ta kawae yake da kallo, ssae take basa sha'awa, kujera ta xauna tace "bari in jira ka a nn" ya gyada mata kai snn ya shiga xuba shinkafar gabansa a plate. Shidda saura ya mike yana kallon Ameesha yace "tashi in kai ki gida dare na yi" ta mike tana gyara mayafin kanta, shi kuma ya nufi sama, dakin Ashnaah ya bude a hankali ya sameta kwance tayi dai dai tana bacci, no wonder yyi mmkin rashin saukowarta, har xae rufo mata kofa sae kuma ya fasa, yana kallonta yace "ke" a firgice ta farka, ta mike xaune da sauri tana kallonsa, ya galla mata harara yace "hka aka koya maki a gidan ku ki dinga bacci da yamma" hamma tayi tana hararansa, snn ta mike tsaye tayi mika ta nufi bathroom abunta ta bar sa nn tsaye, binta yyi da kallo har ta shiga bayin snn ya kulle mata kofar dakin ya sauka kasa, bakin mota ya tadda Ameesha tana jiransa, ya bude motar suka shiga suka bar gidan. Bakwae saura ya ajiye ta a kofar gidan su yace xa su yi waya anjima, tayi murmushinta Mae kyau ta daga masa hannu snn ta nufi gate dinsu, bin ta yyi da kallo har ta shiga snn ya sauke ajiyar xuciya yyi reverse ya bar anguwar ya kama hanyar gidansu, a masallacin da ke kofar gidansu yyi sllh snn ya shiga gida, sama ya nufa ganin bbu kowa a falo ya shiga dakin umminsa, ya sameta xaune kan darduma, sae da ya jira ta gama addu'o'inta snn ya sauka kasa ya gaida ta, ta amsa tana murmushi tace "sae yau Abbana, ina Fateema" yyi murmushi yace "tana gida ummi, rukayya fa" ummi tace "ina jin tana dakinta, daga ina kke hka," yace "daga gidan su Ameesha" Ummi tace "Ameesha kuma, lfya dae ko" yace "lfya ummi ajiyeta nayi ne" ummi bata ce komae ba, can dae tace "to ina fateemar," yace "tana gida nace ummi" "to ya baka taho da ita ba xaka var ta ita daya da magariban nn" shiru yyi bae ce mata komae ba, can yace "Abba na nn" ummi tace "ina ga ya dawo daga masallaci ynxu ka Duba dakinsa" mikewa Khaleel yyi yace "ina xuwa mum" snn ya fita xuwa dakin Abbansa, Abba na canxa channel xaune falonsa da remote a hannu Khaleel ya shigo, wuri ya nema ya xauna nn kasan carpet snn ya gaida dad din nasa, ya amsa yana cewa "kayi wuyar gani son" Khaleel yyi murmushi yace "wllh kam Abba aiki ne ya rike ni" Abba yace "to Allah ya taimaka, ya iyalin ka" Khaleel yace "alhmdllh Abba" hira ssae suka yi da dad din nasa daga bisanni yace "Abba dama wata magana na xo maka da, Allah yasa xaka ban goyon baya" Abba ya tattara hankalinsa gaba daya kansa yace "to ina jin ka son, wace mgnar ka xo da" ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 42.... Khaleel ya dan shafa kansa ba tare da ya kalli Abban nasa ba yace "Dama ba wata magana bace Abba aure nake son kara yi" yana fadin hka ya dago kansa don ganin reaction din dad din nasa, kallonsa kawae Abban nasa ke yi, Khaleel ya sunkuyar da kansa, Abba ya numfasa yace "aure kuma?" Khaleel ya dago kansa a hankali yace "in'sha Allah Abba" Abba yace "lfya dae koh" Khaleel yyi murmushi yace "lfya lau Abba" Abban yyi murmushi yace "to Allah ya bada sa'a, amma ina ka samo matar" Khaleel ya kuma sunkuyar da kansa yace "Ameen Abba, Khadija ce," Abba yace "wace Khadijar" Khaleel xae yi magana Abba yace "au! ko dae yar wajen Alhaji Mukhtar" Khaleel ba tare da ya dago kai ba yace "ita Abba" Abba yyi murmushi yace "ahh ae hkn da kyau Masha Allah, Allah ya tabbatar da alkhairi, amma matar ta ka ta amince dae ko?" Khaleel yace "eh ta sani abba" Abba yace "gud! Allah ya xaba abinda ya fi alkhairi son" Khaleel yyi murmushi yace "Ameen Abba, but plss Abba kae xaka ma ummi magana don bn san ynda xata dauki xancen ba" Abba yace "sam bata da ikon hanaka aure don ko uku kace kana so ynxu in dae xaka yi adalci aura maka xa ayi" Khaleel bae dae ce komae ba yyi murmushi kawae, bae bar falon Abbansa ba sae kusan Karfe tara, don tare ma suka fita masallaci don yin sllhn isha suka dawo suka ci gaba da hirarsu, ummi ce ta shigo falon tana kallon Khaleel tace "kai kasan xa ka jima hka don me xaka bar yar mutane ita daya a gida da daren nn fisabillahi" Khaleel yace "ynxu xan tafi ummi ni ban san ma lkci ya wuce hka ba" tana hararansa tace "ina ko xaka sani" juyawa tayi ta fice daga dakin, Abba yyi murmushi yana girgixa kai, Khaleel ya mike shima yana murmushin yace "Abba bari in je sae da safe" Abba yace "to Allah ya tashe mu lfya" dakin mum dinsa ya shiga yace "to ummi na tafi sae da safe" tace "Allah ya tashemu lfya" murmushi yyi ya juya ya fita ya rufe mata kofar ta, dakin Rukayya ya bude ya sameta kwance tana danna waya, ta mike xaune da sauri tace "lah yaushe ka xo yaya" hararanta yyi yace "me yasa baki xuwa gidana" ta dan turo baki tace "ae ya Khaleel matar nn taka ce bata da mutun ci shi yasa bana son xuwa" yace "gidanta ne ko nawa" tace "to yi hkuri yaya xan xo kila Sunday" yace "Allah ya kai mu," snn tayi Masa sae da safe ya rufo mata kofar ta ya sauka kasa. Karfe goma saura Khaleel ya isa gida, yana shiga falo ya kashe wutan, snn ya nufi sama, har xae bude dakinsa ya shiga sae kuma ya nufi kofar Ashnaah ya bude, xaune ya sameta kasan dakin ta hade kai da gwiwa, ta dago da sauri tana kallon kofar, hawayen dake makale idonta ne ya sauko a hankali bisa kuncinta, ta mayar da kanta bisa gwiwanta, tsayawa yyi yana kallonta, can dae ya karaso Cikin dakin Har lkcb yana kallonta, ya durkusa gabanta bbu yabo bbu fallasa yace "kina da matsala ne" dago kanta tayi da sauri can ta mike tana huci, ta shiga masa wani matsiyacin kallo tace "ikon Allah, halan dae meye gami na da kae da har xaka wani shigo min daki kana neman sanin matsalata???" kallonta ya tsaya yi, can yyi huci me xafi ya kai mata wani wawan mari, bata gama recover ba ya kuma Kai mata wani snn ya turata da karfi ta fadi ta buga kai da gado ya juya ya fice daga dakin, kuka ta dinga rusawa tana rike da kanta tana masa Allah ya isa, tayi mai isarta snn ta mike a hnkli ta hau kan gadonta tana sauke ajiyar xuciya, ranan kwata kwata bata runtsa ba, ga ciwon cikin da ya addabeta tun daxu ga kuma ciwon kan da Khaleel ya daura mata. Da safe tana kwance ta ji fitar motarsa, ta mike xaune da sauri tana tunanin inda xata samu kudi ta ba mai gadi ya je chemist ya siyo mata maganinta don tasan in ba maganin nn ta shiga uku, mikewa tayi da kyar, ta fita daga dakin ta nufi dakin Khaleel, a kulle ta ji shi, ta ja dogon tsaki wato kila jiya ya gane ta shigar masa daki knn, komawa dakinta tayi ta fada kan gado ta shiga rusa kukan takaicin jin mgnr mahaifinta da bata yi ba tun farko, da yasan tana jin mgnr sa da bbu abinda xae sa yyi Mata irin wnn auren masifar, ta ci kukanta ssae daga karshe baccin da bata yi ba jiya ya dauketa, ko da ta farka da rana ko kadan bata da appetite sae taji kmr xaxxabi ke neman rufeta, ta dae samu da kyar ta shiga bayi tayi alwala ta fito tayi sllh snn ta koma ta kwanta, wajajen Karfe hudu ta farka ta dalilin wani axababben ciwon mara, ko ba a gaya mata ba tasan period dinta ne ya xo mata, ta sauko daga kan gadon da kyar ta xauna kasa jin xuciyarta na tashi kmr xata yi amae, kasa daurewa tayi ta fashe da kuka ssae tana yarfe hannu ga shi Meenah bata xo ba, ynxu da gidan su take da tuni an tanadar mata magungunanta tunda an san irin axabar da take sha, ko pad din ma bata da, to wa xata gaya ma, tunanin hkn yasa ta kuka ssae, ta dinga mutsu mutsu a daki ita daya kmr me nakuda, har aka yi isha tana nn xaune ta ci kukanta har ta gode Allah, Karfe tara da kusan rabi Khaleel ya shigo gidan, ya kashe wutan falonsa as usual ya nufi sama xae shiga dakinsa, shesshekar kukanta ya ji, ya juya yana kallon kofar dakinta, ya dde tsaye inda yake daga bisanni ya nufi dakin ya tura kofar, da sauri ta dago tana kallon kofar har lkcn tana xaune inda take, ssae idonta ya kumbura lebbanta suka yi ja sbda kukan da ta ci, kauda kanta tayi, ya karaso cikin dakin ya durkusa gabanta yana kallonta yace "idan kika min mgnr bnxa xan baki mamaki, Meye matsalarki?" bbu yabo bbu fallasa yyi tambayar, tayi shiru ta ki cewa komae fuskarta a daure, tsawan da ya tsoratata ya daka mata yace "ba mgna nake maki ba" ta fashe da wani Sabon kukan tana komawa baya daga xaunen da take tace "ni ka rabu dani bbu ruwan ka" fincikota yyi ta fasa ihu a tsorace tace "wayyo kayi hkuri wllh cikina ke min ciwo" cikin kuka ta karashe mgnr, kasan tiles din dakin taga yana kallo ta sunkuyar da kanta da sauri ita ma don ganin abinda yake kallo, jini ta ga dae dae inda ta bari, juya masa baya tayi da sauri ta kuma saka kuka. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 43..... Kallonta kawae Khaleel ya tsaya yi, ta shiga kkrin mikewa tsaye amma kunya yasa ta kasa, komawa tayi ta xauna ta shiga rusa wani Sabon kukan, ya mike ya xagayo gabanta yana mata wani irin kallo yace "wa kika gaya ma cikin ki na ciwo" kauda kanta tayi bata ce komae ba har lkcn tana kuka, ya hade rae yace "ohh don cikin ki na ciwo shine xaki dinga bata ma mutane waje da kazantar ki, kina hauka ne" cikin kuka tace "to ni nasan inda xan samu abinda xan sa" ya galla mata harara yace "baki gansu cikin kayan akwatin ki ba" ita ma ta galla masa harara tace "to na taba Budewa ne" murmushi yyi ya nufi gun akwatunan lefenta ya shiga bubbude su, ta juya tana kallonsa don tun da ta shigo gidan bata taba bude ko da akwati daya ba a cikin akwatuna shiddan da yyi mata, tana kallo ya ciro pad daya cikin akwatunan da aka xuba kayan shafe shafe da kayan make up, yana rufe jakar ta dauke kanta da sauri, ya jefa mata kan gado ya juya xae fita, da sauri ba tare da ta shirya ba tace "toh cikina ciwo yake min kuma bbu maganin da xan sha" ta karashe maganar cikin kuka tana yarfe hannu, juyowa yyi yana kallonta sae kuma yyi tsaki ya fice daga dakin, kuka ta kuma fashewa da ssae, ta mike da kyar ta nufi bathroom, mop ta dauko da ruwa xata gyara dakinta amma ta kasa don wani axaban ciwo da mararta ke mata ta durkushe wajen ta dinga rusa kuka kmr an aikota, ta kusa minti goma tana abu daya, Khaleel ya bude kofar dakin ya shigo, tsawa ya daka mata yace "wae kina da hnkli kuwa, baxa ki tashi ki gyara jikin ki ba" cikin kuka tace "ni baxan iya ba cikina ciwo yake min" karaso wa kan gadonta yyi ya dauki pad din da ya ajiye mata ya karasa kusa da ita ya mika mata yace "tashi ki bace min a nn" mikewa xata yi amma ta kasa, hkn yasa ya dago ta ya mika mata pad din snn ta nufi bathroom dinta tana ci gaba da kukanta, ko kafin ta fito har ya gyara gun da ta bata, yana xaune gefen gadonta yana hada allura, kallo daya tayi masa ta dauke kanta tayi kwanciyarta kan gadon tare da juya masa baya, yana gama abinda yake ya juya yana kallonta yace "have u eaten" fuskarsa a daure yyi mata tambayar, ba tare da ta jiyo ba ta girgixa masa kai, mikewa yyi ya fita daga dakin, sae gashi ya dawo da ruwan xafi cikin cup, ya xauna inda yake da, ya shiga bude kayan tean da ta jera kan bedside drawernta, ya gama hada tean snn ya bude sugar xae xuba yaji bbu komae ciki, juyawa yyi da sauri yana kallonta don yasan bae ci ace sugarn ya kare ba yace "ina sugarn dake kwalin nn" ta juya ita ma tana kallonsa tace "ya kare mana, sugarn ma da ba xaki" yace "yyi kyau, shine xaki ce min cikin ki na ciwo ko" kin cewa komae tayi yace "rokon ki xan yi ki tashi ki sha tean" mikewa tayi fuskarta a daure ta karaso gabansa ta durkusa ta dauki tean ta shiga sha a hnkli, kallonta kawae yake, ta cire bakinta a cup din ta dago tana kallonsa ya dauke kansa da sauri, ta ajiye tace "ni na koshi" harara ya galla mata yace "shanye ki bn cup dina" ita ma ta hararesa snn ta ci gaba da shan tean, ajiye kofin tayi ta Mike xata bar wajen ya fixgota ta fado kansa ta xamo kasa da sauri, ya mike ya dauki alluran da ya gama hadawa, yana kallonta, xaro ido tayi tace "wae ni xaka ma allura," tsayawa yyi yana kallonta, can ya juya ya fice daga dakin, mikewa tayi ta koma kan gado tayi kwanciyarta tare da Jan tsaki tace "hka kawae sae in bude maka zani ka min allura, ae ba yar iska nake ba, Allah xae sauwake min" kmr xata yi kuka ta karashe mgnr jin wani Sabon ciwon da ya taso mata to yau ya xata kwana da ciwon maran nn, har daya saura Ashnaah bata ga bacci ba, bbu abinda take sae juye juye da aikin kuka kan gadonta don ciwo ya isheta, gani tayi bbu sarki sae Allah ta mike da kyar tana kuka ta fice daga dakin ta nufi dakinsa, yana danna laptop lkci daya yana waya ta shigo dakin, ta xube masa nn bakin kofa ta dinga rusa kuka tana cewa wayyo cikina, ajiye wayar hannunsa yyi yana dariya yana kallonta, ta juya masa baya da sauri taki kallonsa sae kuka take, mikewa yyi ya karasa inda take ya durkusa yana kallonta yace "kina son alluran ynxu" kin cewa komae tayi ganin ya mike xae bar wajen yasa tayi saurin cewa "eh tana share hawayen fuskarta, alluran ya dauko yana kallonta, ta mike a hankali ta nufi kan gadonsa ta yi rup da ciki, tsayawa yyi yana kallonta, can ya karaso ya durkusa kusa da ita ya shiga bude xanin da ke daure kugunta, da sauri ta juyo cikin kuka tace "to ka min a cinya plss" murmushi yyi yace "OK" ta Mike xaune ta bude cinyarta tana kallonsa, kallon cinyar kawae ta ga ya tsaya yi, ta rufe da sauri tana hararansa xata yi magana ta ga ya kuma Budewa ya dauko cotton wool din da ya soma a spirit ya shiga goga mata a hnkli, sae kallonsa take kmr xata yi kuka har wani rawa jikinta yake don tsoro, tana ganin ya dauko alluran ta fasa ihu ta fada kansa tace "Wayyo don Allah kar ka min da xafi plss" ba karamin wahala ta basa ba kafin ya mata alluran, ta dinga rusa masa kuka tana kwance kan gadonsa, yyi tsaki ya fice daga dakin. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 44..... Bayan minti kusan takwas da fitan Khaleel wayarsa ya shiga ring, Ashnaah da ke kwance ta dan samu relief har bacci ya soma daukan ta ta juya a hnkli tana kallon wayar da ke gefenta, jawo wayar tayi tana kallon me kiran ta ga Meesha a gaban screen din, tsaki tayi ta ajiye wayar ta juya, nn da nn bacci ya kuma dauketa. Karfe biyu saura Khaleel ya shigo dakin, kallo daya yyi mata ya dauke kansa ya kulle dakin snn ya nufi inda wayarsa ya ke ya dauka ya ajiye gaban mirror snn ya kashe wutan dakin yyi kwanciyarsa can nesa da ita, amma ya kasa bacci, bayan minti talatin da kwanciyarsa ya ga sae juye juye take, juyawa yyi yana kallonta can ya dauke kansa, jin ta mike xaune yasa ya kuma juyawa yana kallonta, kkrin sauka ta shiga yi daga kan gadon ya kunna bedside lamp yace "me ya faru" bnxa tayi masa ta mike ta nufi bathroom din da ke dakin, yyi tsaki ya kashe wutan da ya kunna, ko da ta fito yana kallonta ta nufi kofa xata fita ta ji kofar a rufe da key, ta juya tana kallonsa kmr xata yi kuka, can dae ta ja dogon tsaki tana hararansa, kasan tiles din dakin ta dawo ta kwanta shi dae bae ce mata komae ba sai rufe kansa da bargo da yyi. Ko da ya tashi da asuba kan gado ya ganta kwance, ya mike ya shiga bathroom don yin alwala. Karfe bakwae khaleel ya fito daga wanka yana goge jikinsa da karamin towel, idonsa ya sauka kan Ashnaah dake kwance hankalinta kwance tana bacci, still yyi yana kallonta, bae taba lura da irin hasken ta ba sae ynxu don fara ce ssae Ashnaah kmr wata balarabiya, kan kafafuwanta da lap dinta masu daukan hnkli ya kuma sauke idonsa, bata da maraba da tsaraici a lkcn don tuni xanin dake jikinta ya kama gabansa, wani kasala ce ta saukan Mae a lkcn, ya karaso kusa da gadon ba tare da yasan yyi hkn ba har lkcn idonsa na kan cinyoyinta, a hankali ya kuma sauke idonsa kan kirjinta yana kallon abinda ya kuma girgixa shi, waow kadae ya iya furtawa a xuciyarsa ba tare da ya ma san yyi hkn ba, yar rigar bacci silk ne ja jikinta mae bra da yyi mugun haska fatan ta, karasa wa yyi kmr wani Mara lfya ya duka dae dae kusa da ita yana kallon kyakkyawan gentle face dinta da jan lips dinta, hannu ya daura a hnkli kan kirjinta yana shafa wa, wani irin shock ya ji, ya mike da sauri kmr wnda ya tuna abu ya bar wajen bae kuma kallon inda take ba, ko minti goma cikakke ba ayi ba ya gama shiryawa ya dauki makullin motarsa ya fice daga dakin kmr ana hankada sa. Yana xaune office wajajen sha biyu yana Duba aikin gabansa duk da ko kadan hnklinsa baya Kansu Najeeb ya shigo office dinsa, daga kai yyi yana kallonsa, Najeeb ya cire gloves din hannunsa ya jefar cikin waste bin din dake office din snn yyi kwanciyarsa kan gadon da ake Duba pregnant women dake office din, yace "ni hutu nake son dauka wllh duk na gaji da aiki now adayz" ya Mike da sauri yana kallon Khaleel yace "yauwa ka je kiran mum din taka, hope dae ta yadda, don ban son abinda xae raba ku da Ameesha" Khaleel ya ajiye pen din hannunsa ya sauke ajiyar xuciya yace "sae anjima da daddare xan tafi" Najeeb yace "ko dae shi ne ke bother dinka hka tun safe, c'mon chill guy ba dole ma ta amince ba tunda Abba ya amince" Khaleel yace "No ni ba ma shi ke bother na ba wllh, ka gane ko Najeeb," sae kuma yyi shiru yace "ko da yake ma forget don ka fiye rainin hnkli" Najeeb yace "haba dae ae ni bna rainin hnkli a serious issues ina jin ka" Khaleel ya dan shafa sajensa yace "kan yarinyar nn dake gidana ne" sae kuma yyi shiru, Najeeb yace "Wat abou her?" Khaleel yace "I donno frnd, na kasa mata abinda nayi niyya tun farko, nd I married her for dat purpose gashi ko kadan bata raga min still a gidan nawa, bata da kunya ko kankani ga ta yarinya yar karama... Yhu knw get wia am heading mana guy" Najeeb ya fashe da dariya ssae, Khaleel ya hade rae yana kallonsa, sae da yyi me Isar sa snn yace "yhu c garin neman kiba ka kwaso ma kanka rama, wat I notice in here is dat ka fara sonta knn tunda har ka kasa mata abinda yasa ka Aurota, kuma kace ba raga ma tayi ba a gidan naka stil den me kke yi da ita har ynxu, kae ba hutawa kke yi da ita ba, kai ba aikin komae take maka a gida ba, kace bata respect din ka kuma, to wae ma da me kayi niyyan mata ne tel me pls" Khaleel ya mike yana masa wani irin kallo yace "amma ko da ka cuce ni in har ka bude baki kace ina son yarinyar nn, kasan Allah? Wllh wllh dai dai da rana daya ban taba jin ko da digon son wata mace a xuciyata ba a duniya, mata masu class I mean big big babes da suka san duniya duniya ta sansu ban so su ba sae wnn kwailar, yaushe ma aka haifeta? she is just seventeen fa, yaushe ta balagan ma da har xa a so ta infact, ni koh tausayin rayuwarta ma kawae nake wllh, tausayi take ban don har yau naga alamar bata san meye life ba yarinyar" Najeeb yyi dariya yace "to tunda har ta fara Baka tausayi snn kai kasan ba sonta kke ba wats d need of keepn her in ur home, just let go of her, in ana ramawa a lahira ka rama abinda tayi maka a can, tunda kayi repent har kasan meye tausayi" dariya ssae Najeeb yake, Khaleel kallonsa kawae yake yana huci, hkn yasa Najeeb ya danne dariyarsa, Khaleel ya ko ma ya xauna xuciyarsa na tafarfasa, Najeeb ya shafa kansa yace "kaga joke apart Khaleel ka sake ta kawae ta koma gidan su ae ko ba komae da baxawara xa a kirata" Khaleel ya girgixa kansa yace "impossible" Najeeb yace "I don't get dat, to kace tausayinta kke, den y nt let her go, meye amfanin ajiye ta a gidan ka bata tsinanaka da komae, kila da ma nine xan dan dinga maneji ina hutawa da ita har lkcn da xata gundure ni nd den I send her out, ko ba komae na mayar da ita baxawara, to kai wnn ko ka saketa ma ae jin ddi xata yi tunda ka bar ta da budurcinta, kai gashi sugar xata yi tunda budurwa ce kuma yarinya" Najeeb ya karashe mgnr yana dariya, Khaleel ya hararesa, Najeeb yace "no joke apart, ynxu xaka ce ba ka sha'awanta" Khaleel ya sauke ajiyar xuciya tare da shafa kansa ya ki ce masa komai. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 45..... Najeeb yyi dariya ya dawo kusa da abokin nasa jin yyi shiru, ya tsaya yana kallonsa yace "ya kayi shiru frnd" Khaleel ya dago kansa yana hararansa yace "infact ehh ina sha'awar nata, to tsoron ka xan ji da baxan gaya maka ba" dariya ssae Najeeb yake har da dafe table, Khaleel sae kallonsa yake kmr ya shakesa, Najeeb ya dago kansa bayan ya ci dariyarsa yace "to don me xaka dinga wahalar da kanka hka Khaleel, just enjoy ur self frnd, kayi ynda ka ga dama da ita, after all ae matar ka ce," Khaleel na masa wani irin kallon yace "amma kai din nn baka da meaningful advice wllh, hka kawae ka ja yarinya ta raina ni, to ni ko desire xae kasheni me xae kai ni gun kucakar yarinyar nn, plss ka san irin mgnr da xaka dinga min mana" Najeeb yace "amma kuma kke sha'awarta, look ba wae nace ka je ka lallabata ka huta da ita bne, no of course ita wacece da xaka lallaba don uwarta, I mean ta karfi xaka je mata ko ta yrda ko bata yrda ba if it means rapin her just go on, enjoy ur self to d core nd leave mehn, dama ga ta karamar yarinya kuma virgin I guess, ba karamin honey xata yi ba, nd bet me daga ran da ta ji ka wllh tsoron ka xata dinga yi duk wnn tsiwan da fitsara xaka neme su ka rasa, wae ina ma ni ne wllh," kallon bnxa kawae Khaleel yake masa, da mmki Najeeb yace "ohh wae kae da don kawae ka rama abinda tayi maka kmr ynda naji kana yawan boost unnecessarily har ya kuma bn ga wani irin ramuwar da xa a yi ba bn kuma ga alama ba ka Aurota kawae, to daga baya kuma sae ka saketa ta tafi da virginity dinta ko me, tabdi" Khaleel ya sauke ajiyar xuciya yace "I've heard" Najeeb yace "xaka yi ynda nace maka knn" Khaleel yace "yep may b" Najeeb yace "yauwa frnd pls kayi hkn ka fidda rai ni, kuma kar ka tausaya mata ko kadan" bae jira me Khaleel xae ce ba ya mike daga xaunen da yake yace "bari in koma office xa mu hade ltr" bin sa kawae Khaleel yyi da kallo har ya fita snn ya sauke ajiyar xuciya ya ci gaba da abinda yake. A hankali Khaleel ya tura kofar dakin umminsa ya shiga da sallamarsa snn ya kullo mata kofar, waya ya sameta tana yi, hkn yasa ya nemi gu ya xauna har ta gama snn ya sauko kasa ya gaida ta, ta amsa ba tare da ta kallesa ba, komawa yyi gefen gadonta ya xauna yace "kin yi kirana ummina" ta galla masa harara tace "sae ynxu ka ga daman xuwa" yyi murmushi yace "ba hka bne ummi, ynxun ma daga aiki nake wllh" bbu yabo bbu fallasa tace "wani xancen ka xo ma da Abbanka rannan Khaleel?" Khaleel yyi shiru yana kallonta snn ya sunkuyar da kansa yace "Ca nayi masa aure xan yi ummi." ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 46.... Ummi ta dake tana ci gaba da masa mugun kallo tace "akan wani dalili?" Ya dago kai yana kallonta xae yi magana ta rigasa tana girgixa kai tace "to bn amince ba, in kuma bn isa da kai ba sae ka nuna min ynxu in ga, tashi ka ban waje" kallonta kawae yake ya ma rasa me xae ce mata, a fusace tace "to ko dukana xaka yi irin wnn kallo hka, bn da ka raina mutane kwanan ka nawa da yin auren nn, salon ka ja mana magana a gari yarinya karama na xaman ta lfya ka tashi ka ce xaka kawo mata abokiyar xama ku hadu kuyi ta cutan ta ko, to baka isa ba Khaleel kayi kadan, in kanwarka aka yi ma hka xaka ji ddi, plss leave malam" Khaleel ya kuma sunkuyar da kansa yace "to amma ummi naga da amincewarta xan kara auren kuma wnn abun naga ba haramun bne bare..." Wani tsawa ta daka masa ta mike tana huci tace "don uwarka ni xaka kawo ma wnn mgnr, to in ka isa ka je kayi auren muga, get out in daina ganin ka a dakina, Mara tunani kawae" mikewa Khaleel yyi yana shafa kansa bae kuma cewa komae ba ya nufi kofa xae fita Abba ya shigo dakin, yana ma ummi mugun kallo yace "sannu Fateema kin yi kokari, kmr ynda ki ka hanani kara aure shine da na ma xaki hanasa to wnn ne kuma baki isa ba, auren sa bbu fashi ni nayi wnn alkawarin" Khaleel yace " A'a Abba bae kai ga hka ba, tunda bata so kawae ni na fasa wllh, bana son abun da xae bata ran ummi na, a bar maganar auren kawae" wani kallon bnxa Abba ke masa yace "sannu me uwa, wato ni xaka watsa ma kasa a ido na xo tare maka bakin rai koh, yyi maka kyau" ficewa Abba yyi daga dakin, Khaleel yyi murmushi ya dawo kusa da umminsa dake xaune ko kallon inda mai gidan nata yake bae yi ba, ya durkusa kusa da ita a hankali ya fara mgna "kiyi hkuri ummina idan na bata maki wllh na bar batun auren tunda ba ki so, kila hkn ne yafi alkhairi, ki kwantar da hankalin ki ummi na rufe xancen daga nn wllh" ummi ta dago tana kallonsa tace "Ka kawo min fateemar gobe sae in ji ko da gsken da amincewarta, in tace ehh, to baxan hanaka auren ka ba tunda ga abinda uban ka ke cewa a kaina, in kuma tace bata san da xancen ba to ko me xae faruwa baxa kayi auren ba" Khaleel ya girgixa mata kai yace "No ummi ni na bar mgnr auren wllh na hkura" ummi tace "ni ka tashi ka bn waje kayi abinda nace maka bana son mgna" ya dan Marairaice mata yace "wae ummina fushi kika yi da ni, wllh har xuciyata na fasa" ummi ta dan sake ranta ta shafa kansa tace "kar ka damu Khaleel kayi ynda nace maka kawae, ni bnyi fushi ba" mikewa yyi yace "to shknn ummi ngd, Bari in tafi gida dare yyi" tace "to Allah shi kiyaye" sae da yyi ma Abbansa sallama snn ya fice daga gidan yana murmushin irin amsawan da Abban yyi masa. Karfe tara da rabi Khaleel ya shiga gidansa, kashe wutan falon yyi as usual ya nufi sama ya bude falonsa a hnkli ya shiga yana kallon kofar dakinta, bedroom dinsa ya nufa ya tsaya da mmki yana kallon dakin, ynda ya fita ya bar shi hka ya dawo ya same shi sae dae bata kan gadon ynxu, ya fice a fusace ya nufi dakinta ya bude ya shiga, bata dakin jin xuban ruwa da kamshin soap ya gane wanka take, tsayawa yyi a dakin yana jiran fitowarta fuskarsa a daure, ta fito daure da tawul tana saka gashinta cikin net din hannunta, sosae ta tsorata ganinsa tsaye a dakin don bata ji shigowarsa ba, ta juya da gudu ta koma bayin tana cewa"Innalillahi, kai ni nashiga uku da wnn jaraba, don Allah ya xa ka ke shigo ma mutane daki hka bbu neman izini, ynxu da ban daura tawul ba fa" kallon kofar bayin kawae yake fuskarsa a daure har lkcn, ita kuma har lkcn bata daina mitan da take ba tana jaraba, ya karasa bayin a fusace ya tura kofar ta koma baya a tsorace kan ta ce komae ya fixgota ya shiga kunce tawul din jikinta da karfi duk da irin ihun da take jikinta na rawa tana basa hkuri tana cewa bbu komae jikinta, hkn bae hanasa kunce wa ba snn ya fixge da karfi daga jikinta ya jefar cikin bedroom dinta. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 47..... Ashnaah ta fashe da kuka ta duka da sauri tana kare kirjinta da hannunta, ssae ta tsorata don tun da take bata taba tsayawa hka gaban namiji ba don ma Allah ya taimaketa kirjinta kadae ne waje, shi kam kallonta kawae ya tsaya yi, taki dago kanta sae kuka take tana cewa don Allah yyi hkuri ya fita plss, dukawa yyi har lkcn yana Mata wani irin kallo snn ya dago ta da karfi ta inda xae iya kallon abinda take boyewa da kyau, ta fashe da wani sabon kukan jikinta na rawa ta shiga kkrin kare kirjinta kuma amma yaki sake hannunta, tsaf ya shiga kare ma kirjinta kallo, cikin wata kasalalliyar murya taji yace "me gare ki a nn da kike boye min, tel me wats dia" kasa dago kai ta kallesa tayi har lkcn bata daina kukan da take ba, jinginar da ita yyi jikin bayin ya dago kanta yana kallon cikin kwayar idonta da nasa idon da ya kada lkci daya, ta rumtse idonta da sauri har lkcn jikinta na bari, cikin rawan murya ta shiga cewa "don Allah don annabi kayi hkuri ni bn san kai bne ka shigo dakin shi yasa nayi mgna plss kayi hkuri wllh baxan sake ba" cikin kuka ssae ta karashe mgnr, Khaleel kam ko kadan bae san abinda take cewa ba don idonsa na kan abubuwan da suka dagula masa lissafi lkci daya, ya kasa daina kallonsu, maganganun Najeeb kadae ke masa yawo a ka a lkcn, saukan numfashinsa taji a wuyanta snn lebbansa duk a lkci daya, ta bude ido a tsorace xata bara ihu ya matse ta jikinsa ya toshe mata baki da hannu daya snn ya xamo fuskarsa a hnkli xuwa kan kirjinta, Ashnaah da ta ji kmr numfashinta xae dauke don tsabar tsoro ta shiga kiciniyar kwace kanta a hannunsa jikinta na rawa amma ta kasa, wani ihu ta fasa masa a gigice ganin abinda yake yi, bata gama rufe baki ba taji bakinsa cikin nata, ya shiga mata kiss me dagula lissafi, daga ita har shi kasa tsayuwa suka yi duk suka xube nn kasan bayin, daga jin irin numfashin da take yasan ba karamin tsoro taji ba amma duk da hka bae kyaleta ba sae da ya ga jini na silalowa kasan kafarta sae a snn ya tuna al'ada take, ya turata ya mike da sauri ya fice daga bayin ya nufi dakinsa da kyar ya fada bathroom, Ashnaah ta fashe da wani sabon kukan har lkcn jikinta na rawa don ba karamin tsurewa tayi ba, ta kusa awa daya tana abu daya snn ta mike da kyar ta gyara jikinta ta dauki wani tawul din ta daura ta fito dakinta a sanyaye rigar baccinta kawae ta xura ta kwanta kan gadonta a hankali tunani kala kala na mata yawo a ka, to wae me Khaleel din nn ke nufi da ita ne xae dinga mata iskanci hka, fitar motarsa ta ji daga gidan ta mike da sauri ta nufi window amma tuni har ya fice, ta ja dogon tsaki don wani mugun tsanarsa fiye da na da take ji a xuciyarta, kan gadonta ta koma tayi kwanciyarta tare da jan bargo har lkcn gabanta bae daina faduwa bs. Ashnaah na tashi da asuba ta nufi window don ganin ko ya dawo amma bata ga motarsa ba, ta tabe baki ta koma tayi kwanciyarta don ba sllh take ba. Da yamma Ashnaah na kwance dakinta tana tunanin ko me ya hana Meenah xuwa har ynxu taji an bude kofarta ta Mike da sauri don tasan ita kadae ce a gidan, ya tsaya daga bakin kofar fuskarsa a daure yana kallonta, kasa kallonsa tayi ta koma tayi kwanciyarta ta juya masa baya, jin takunsa cikin dakin yasa ta kuma mikewa xaune da sauri kmr xata yi kuka tana kallonsa, ya daka mata tsawa yace "tashi ki dauko hijab din ki" mikewa tayi a hnkli fuskarta daure ta bude wardrobe dinta ta ciro hijab ta saka, karasowa kusa da ita yyi yana mata mugun kallo ya fixgota ya hade ta da bango yace "ki saurari abinda xan gaya maki da kyau." Kae kawae take gyada masa a tsorace don ta gama tsorata da shi tun jiya da daddare. Make Una no vex bacci ne a ido na wllh. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 48..... Khaleel ya sake ta ya koma baya yana mata wani mugun kallo yace "duk xancen da ummi na xata maki kar ki kuskura ki nuna mata baki san da xancen ba , da bakin ki nake so ki ce mata ae kin amince, ki ka kuskura kika hada ni da ummina sae na maki abinda baki taba tunani ba a rayuwarki, just dare me ki ga" Kallonsa kawae Ashnaah ke yi tana mmkin to wani xance ne wnn xata ce ta sani bayan bata sani ba, har ya juya xae bar dakin sae kuma ya dawo yana kallonta yace "in fact aure Zan yi ke wacece da xa a boye ma, ko kin isa ki hanani ne" shiru Ashnaah tayi tana kallonsa, sae kuma tayi murmushin da ya bayyana fararen hakoranta lkci daya ta saka dariya tana kallonsa tace "to ni kuma a su wa xan hanaka aure, Allah ya bada xaman lfya, nima Allah ya ban miji na gari in yi auren" xaro ido yyi yana kallonta yace "me kika ce" duk da ta tsorata hkn bae hanata mgna ba tace "Ca nayi ni ma Allah ya bn miji na gari in yi auren" buge mata baki yyi yace "da auren nawa a kan ki kike fadin hka a gabana?" Shiru tayi bata ce komae ba hannunta a bakinta da ya buge tana kallonsa, yyi kwafa ya fice daga dakin ta rakasa da harara, sae da taji saukansa a stairs snn tace "Allah ya Isar min, in sha Allahu kmr ynda xaka yi aure ni ma sae nayi don ni har yau ba matar aure bace, kuma xaka sha mmki na Yau" ficewa tayi daga dakin ta bi bayansa kar ya dawo ya kwakkwade ta tasan xae aikata, front seat ta bude ta shiga, ya tada motar suka bar gidan, biyar da kwata Khaleel yyi parkin a compound din su, ya bude motar ya fita ya nufi cikin gida ba tare da ya ko kalli inda take ba, ta ja tsaki ta bude ta fito ta bi bayansa tana hararansa, bbu kowa falon sae tv dake faman aiki, tayi xamanta kan kujera shi kuma ya nufi sama, a stairs ya hadu da umminsa xata sauko, ya gaisheta snn suka sauko kasa a tare, Ashnaah da ke xaune falo ta gaisheta kan ta a sunkuye ummi ta amsa da fara'arta tana tambayarta ya gida, har kusan magrib Ashnaah sae xuba kunnuwa take taji xancen da ummi xata mata amma shiru, sae hira take da Khaleel, ita kuma sae kallo take, mikewa tayi daga karshe tana kallon ummi tace "momy Rukayya na sama ne" Ummi tace "eh tana sama bata jin ddi ne" Khaleel yace "me ya sameta ummi," ummi tace "xaxxabi ne kawae, ta ma ji dama dama ynxu" Ashnaah tace "bari in Duba ta" snn ta nufi sama da sauri ta bude dakin Rukayya ta shiga, xaune ta sameta tana rubutu, Ashnaah ta dan daure fuska tace "wayar ki xa ki ara min" nuna mata wayar Rukayya tayi ta ci gaba da abinda take, Ashnaah ta nufi gaban madubinta ta dauki wayar tace "kina da nmbr Meenah" Rukayya tace "ehh" Ashnaah tace "da me kika yi savin" ba tare da Rukayya ta kalleta ba tace "Amina sister" Ashnaah ta Duba ta ga nmbr, bbu bata lkci tayi dialing bugu biyu Meenah ta daga, Ashnaah tace "Haba Meenah shine xa ki min wlknci ki ki xuwa ina ta baxa ido koh" Meenah tayi dariya tace "yar gari kin fito yau da mijin naki knn, wllh ke dae in gaya maki momy ce tace bbu inda xa ni kwana biyu bbu abinda nasa gaba sae yawo, amma kar ki damu kila gobe ko jibi in xo ga wayar ki nn na siya tun ranan" Ashnaah ta washe hakora tace yauwa kawalli nagode ina nn ina jiran ki, sallama suka yi Ashnaah ta katse kiran ta ajiye mata wayar nn inda ta dauka snn ta fice daga dakin. Karfe takwas da rabi tana xaune dakin ummi suna kallo bayan ta gama cin abinci Khaleel ya shigo dakin, ya xauna yana kallon umminsa yace "ga ni ummi" ummi tace "dama nace sae a gabanka xan yi magana da fateema" bae ce komae ba ta juya tana kallon Ashnaah tace "fateema wae da amincewar ki xae yi aure" Ashnaah ta daga kai tana kallon Khaleel taga wani irin mugun kallo yake mata, ta sunkuyar da kanta da sauri kmr xata yi kuka tace "ehh toh momy sae daxun nn yake gaya min wae duk xancen da xa ki min in mun xo gida in ce ehh na sani kuma ae na amince idan ba hka ba wae sae yyi min abinda ban yi tunani ba," ta fashe da kuka tace "wllh momy ban san ashe aure xae yi ba, bae gaya min ba" ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 49...... Khaleel ya kasa daina kallon Ashnaah da taki kallon inda yake, duk da bae yi wani mmkin abinda tayi ba yasan xata iya aikata fiye da hkn dama, da kyar ya iya maida dubansa ga Ummi ya ga kallonsa kawae take, ya sunkuyar da kansa, ummi tace "to tashi ka bar min dakina" bbu musu ya mike yana kallon Ashnaah ya fice daga dakin, sae a snn Ashnaah ta dago kanta tana kallon ummi, kmr xata yi kuka tace "momy dukana fa xae yi in mun koma gida wllh, ki ce ya bar ni a nn" da mmki ummi tace "duka kuma?" Ashnaah ta gyada mata kai, ummi ta ma rasa me xata ce mata can dae ta mike ta fice daga dakin, Ashnaah ta bi ta da kallo tana murmushi. Goma saura ummi ta dawo dakin har lkcn Ashnaah kallo take, ummi tace "tashi ki dauki hijab din ki ku wuce gida" Ashnaah ta dan xaro ido tace "gida ynxu, na tsamman a nn xa mu kwana ae" Khaleel ne ya shigo dakin yana kallon Ashnaah yace "tashi mu wuce ke nake jira" Ashnaah ta juya da sauri tana kallon ummi kmr xata yi kuka, ummi tace "gobe xa da safe xa ku dawo" mikewa Ashnaah tayi ta dauki hijab dinta ta sa, tuni gabanta ya soma faduwa, tayi ma ummi sae da safe ta fice daga dakin ya bi bayanta. Har suka isa gida Khaleel bae ce mata komae ba, har karkarwan sanyi ta shiga yi don tsoro amma ko kadan hkn bae nuna a fuskarta ba, sae da ya jira ta fito snn ya kulle motarsa ya nufi cikin gida ta shiga jan kafarta da kyar tana bin sa a baya, oh ko wani irin duka kuma xae mata yau, kin shiga falon tayi ta tsaya daga bakin kofa tana kallonsa fuskarta daure, bae ma san tana yi ba din jira kawae yake ta shigo ya rufe kofar sa, ganin bata shigo ba ya sa ya daga kai yana kallonta, dauke kanta tayi da sauri still ta ki shiga falon, ya juya ya nufi stairs kawae ya haura sama, ta kusa minti talatin bakin kofar taki shigowa falon ga wani mugun bacci da take ji, daga karshe dae ta gaji don kanta tayi shahada ta shiga falon kmr xata yi kuka ta rufe kofar ta nufi cikin falo ta xauna, har bacci ya samo dauketa daga xaunen da take taji kmr motsi kusa da ita ta mike tsaye a tsorace ta gansa a gabanta ya duka, da sauri ta bar wajen ta ga remote din dake kan kujerar da take ya dauka snn ya mike tsaye yana kallonta yace "ni bani da lkcn ki ynxu, i mean ban gama gather din tym dinki ba" kashe tv dinsa ta ga yyi snn ya kashe wutan falon ya nufi sama ta bi sa da kallo snn ta yi murmushi a xuciyarta tace ko dae momy tace kar ka taba ni ba, sama ta nufa xuciyarta fal murna ta bude dakinta ta shige. Washegari da safe Khaleel ya kai ta gida gun Ummin sa kmr ynda ta umarce shi, bbu yabo bbu fallasa ta amsa gaisuwarsa ya juya ya fice daga dakin, ummi na kallon Ashnaah tace "kina ji na fateema, ki kwantar da hankalin ki, in dae har ina Raye a doron kasa baxan taba barin Khaleel ya walakanta ki ba, ki kyalesa yyi auren sa kar ki tada hankalin ki kin ji" da mmkin ummi sae gani tayi Ashnaah tayi murmushi ssae tace "to momy dama ni bn daga hnklina ba" Da rana Khaleel ya xo tafiya da Ashnaah gida, ko kadan bae ji ddin irin ynda umminsa ke amsa masa gaisuwa ba, Ashnaah tayi ma Ummi sallama ta sa hijab dinta ta bi bayan Khaleel, yana gama parking a gida ya bude motar ya nufi cikin gida ba tare da ya tsaya kulle wa ba ya bar ta nn ciki. Washegari lahadi yana kwance dakinsa idonsa lumshe kmr me bacci ya ji an danna bell, ya mike xaune yana kallon agogo ya ga goma da kusan rabi to waye kuma wnn, tashi yyi ya fita daga dakin don xuwa ganin Wanda ke bakin kofar. Najeeb ne tsaye yana kkrin kiransa, Najeeb yace "bacci kke ne" Khaleel yace "aa na tashi tun safe" hanya ya basa ya shigo falon snn ya shiga tambayarsa daga inda yake, Najeeb yace "gida mana" Ashnaah ce ta fito daga kitchen sanye da dogon rigan baccinta har kasa pink colour me tsantsi, gashin nn nata me kyau na daure da ribbon baki, hannunta rike da cup din tea, Khaleel ya juya da sauri da kuma mmki yana kallonta don bae san tana kasa ba da baxae bude kofar ba, kallonta kawae Najeeb yake ko kiftawa baya yi, wani irin tsawa da ya raxanata Khaleel ya daka mata ba tare da yasan yyi hkn ba yace "me ya sauko dake nn" tsayawa kallonsa tayi kmr wata sha sha sha don ita dariya ma ya bata, Khaleel ya juya yana kallon Najeeb da har lkcn bae kifta ido ba yana kallon Ashnaah, a fusace Khaleel yyi kanta, ta fasa ihu ta juya xata koma kitchen da gudu, ya cafkota don tsabar tsoro hka ta sake cup din hannunta tana kwala ihu, janyeta yyi daga wajen da sauri ganin cup din ya tarwatse da ruwan tean ciki, bata ankara ba taji ya dauketa kmr wata yar bby ya nufi sama da ita, dakinta ya bude ya jefata ciki yana nuna ta da dan yatsa yace "wllh wllh kika sauko min falo sae na kusan fasa maki kai" bae jira me xata ce ba ya fice daga dakin ya sauka kasa, sae a snn Najeeb ya sauke ajiyar xuciya ya xauna, Khaleel ya hade rae ya nufi kitchen ya dauko broom da packer don kwashe kwalaben da ke kasan falon, sae da ya gama tidy din wajen snn ya xauna yana kallon Najeeb yace "ya aka yi guy any prblm" Najeeb ya sauke ajiyar xuciya yace "wae wnn ita ce yarinyar Khaleel" Khaleel xae yi magana ya ji muryar Ashnaah a bayan su. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar50....Mikewa Khaleel yyi ya bude baki da mmki yana kallonta, rasa ma me xae ce mata yyi, to wae ita wnn wace irin mutum ce, tambayar da yyi ma kansaknn a xuciyarsa yana ci gaba da kallonta, ta galla masa harara tace "to wae sbda kayi bako sae in ta tsayawa da yunwa baxan nemi abinda xan sa a cikina ba" Najeeb ya fashe da dariya har da kyakyatawa, a fusace Khaleel yyi kanta kan tayi tunanin gudu har ya kamata ya kuma komawa sama da ita ya bude dakinsa ya tura ta ciki da karfi snn ya kulle dakin ya jingina jikin bango ya dafe kansa, yana tunanin shi kam me xae ma yarinyar nnya ji ddi bnda Wanda yyi niyyar mata da, yana ji tanarusa kuka tana bubbuga kofar ya juya ya sauka kasa, Najeeb yace "haba doctor, ka barta tayi harkangabanta mana, me ta tsare maka a nn, ko kuma in ce me ta tsare mana" kallon bnxa kawae Khaleel ke masa, can ya ja tsaki yace "look, idan bbu takamaiman abinda ya kawo ka ka tashi ka bar min gidana in tafi in kwanta pls" Najeeb ya hade rai yace"ka ga fa wlkncin ka ke hadani da kai wllh, is there anything wrong with my coming here? Sae in tashi in bar maka gidan ka malam" Khaleel ya dan yi murmushi yyi kwanciyarsa kan 2sitter din da yake xaune yace "to Allah ya baka hkuri" Najeeb yace "to ynxu dae wnn ita ce yarinyar da ka aura" Khaleel yace "yeah" Najeeb ya dan yi shiru snn yace "kayi ynda nace maka?" mikewa Khaleel yyi da sauri ya xauna yana kallonsa yace "look ni fa bbu abinda xanbari ya shiga tsakaninmu, ni dae nasan I only romance her once or twice, ta min yarinya da yawa nd beside wahalar da kaina kawae xan yi, in ma ka ga nayi sha'awarta to I saw half naked ne amma hka kawae bata bn sha'awa, ka bar big gals irinsu Ameesha da sauransu" Najeeb ya dan shafa gemunsa yace "to ka saketa Khaleel, stop wasting ur tym wllh" Khaleel yace "dats d lst thing I wil do onearth a ynxu dae" Najeeb bae kuma cewa komae basae tsakin da yyi. Karfe sha biyu da rabi Najeeb ya bar gidan, Khaleel ya rakasa har gun motarsa snn ya dawo ya nufi dakinsa ya bude ya tura a hnkli ya shiga, kwance ya sameta kan 3sitter ta juya baya a falo, ya karasa kusa da ita a hnkli ya duka yana lekan fuskarta don duk a tunanin sa bacci take, ido hudu suka yi ya koma baya da sauri ta mike xaune fuskarta a daure tace "meye kke wani lekana" daukekai yyi ya nufi kofar falon ya bude yana nuna mata waje yace "xo ki fita" mikewa tayi ta fice daga dakin kmr xata tashi sama ya bita da kallo har ta sauka kasa snn ya dan yi murmushi ya kulle dakinsa. Washegari Ashnaah na kitchen da rana tana girka shinkafa da miyar da xata ci, sae gunguni take ita daya a kitchen kmr xata yi kuka tana cewa ni dae nagaji da wnn wahalan yaushe rabon mutum da ya ci nama kullum abinci lami to Allah ya Isar min tunda ba hka ake yi a gidan mu ba naga, jin an bude kofar falon yasa tayi shiru tana sauraro taji wnda xae shigo, shirun da taji yasa ta dan leka falo taga Meenah tsaye, da sauri ta fito tana washe baki tace"lahh ashe ke ce Meenah sannu da xuwa" Meenah tace "baya nn dae koh? Don bn yrda da masu gadin nn ba" Ashnaah tayi dariya tace "baya nn wllh" Meenah ta xauna nn tsakiyar falon ta shiga bude Jakarta ta ciro kwalin wata yar karamar waya me kyau techno, da dan envelop fari karami tace "ga wayar da na siyo maki, wnn kuma maganin da kika tambaya ne gashi" Ashnaah ta galla mata harara tace "bayan har na gama period din ma, ae mutuwa kadae ne bnyi ba wllh" Meenah tace "eyya, wllh momy ce ta hanani fita, ki ce daurewa kawae kika ta yi" Ashnaah tayi dariya tace "yayanki ne yyi min allura wllh" Meenah tace "Ahh anyi abun arxiki su Khaleel" Ashnaah tayi dariya ta dauki wayar tana dubawa tace "amma yana da kyau wllh, bari in dauko nmbr mu gwada kira, kin dae sa min kudi koh" Meenah tace "ke Zeenat fa ta koma gidansu tun shekaranjiya" Ashnaah ta dafe kirji tace "ki ce wllh" Meenah tace "wllh kuwa, bn san ynda suka yi ba ni ma, duk bin kwakkwafi na ban gano komae ba wllh" Ashnaah da har jikinta yyi sanyi ta maxa tace"to ae bae baci ba, still sae na kirasa wllh, ae baxae san khaleed din ne ya sace yar sa ba" Meenah ta fashe da dariya tace "ke khaleel sunansa ba khaleed ba" Ashnaah tace "ayyo" bell suka ji an danna duk suka mike a tsorace lkci daya tace"waye?" Murya masu gadi taji, Ashnaah tace "ya aka yi?" Suka ce kaya ne oga yace a shigo da, Meenah tace "ya dawo ne" suka ce "ehh" sama ta nufa da gudu har tana faduwa, Ashnaah ta dauki wayarta da sauri ita ma ta nufi sama don ta boye, sae da ta boye snn ta sauko ta bude masu kofar ta ga akwatuna hudu a bakin kofar, dae dae lkcn da Khaleel ya karaso balconyn yace "ku shiga da su mana" waje ta basu suka shiga da akwatunan tana binsu da kallo, Khaleel ma ya shigo falon yana bin ko ina da kallo yace "me ke konewa hka" da gudu Ashnaah ta nufi kitchen tana cewa "innalillahi wa inna ilai hi raji'un" ya bi ta a baya da sauri, tana shiga kitchen din ta fasa wani ihu bayan ta sauke miyar ta durkushe kasa da sauri tana ci gaba da ihun, ba karamin tsorata shi tayi ba ya durkushe gabanta ya dagota duk a tunanin sa abu ne ya shiga idonta, a rude yake tambayarta "menene?" Kin bari ya daga fuskarta tayi, yace "wait don Allah ki gaya min me ya shiga idon" da kyar ta bari ya daga kanta,yana kallon idonta da ko digon hawaye bbu yace "to me ya shiga idon" kmr xata yi kuka tace "miyar da na sha wahala nayi ya kone" ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 51..... Kallonta kawae Khaleel ya tsaya yi, ta xame jikinta daga rikon da yyi mata ta shiga komawa baya a hankali tana hararansa, mikewa yyi a fusace yyi ball da ita ya fice daga kitchen din, dariya ta saki har da kyakyatawa tana bin sa da kallo snn ta mike, sae kuma ta ja tsaki ita ma ta fice daga kitchen din, falo ta same sa yana kwantar da akwatunan da masu gadin suka ajiye cikin falon, ta karaso cikin falon tana kallon akwatunan, ba tare da ya kalleta ba fuskarsa daure yace "gashi nn kayan fadar kishiya, ba don kin isa na maki ba sae a bisa umarnin mahaifiyata" murmushi kawae Ashnaah take har da washe hakora, ya dago yana kallonta ganin abinda take yasa ya tsaya kallonta, ta dan tabe baki tana daga kafada tace "ni na yafe, ka kara ma warce xaka aura kawae" tsawa ya daka mata yace "to ki xo ki sani nayi hkn" tace "to dolene? Nace bana so ko" ta karashe mgnr tana hararansa, ficewa yyi daga falon don xuwa gun masu gadi ya sa su kwashe akwatunan su mayar masa su cikin mota, takalma ya gani bakin kofar, da mmki yake kallonsu, can dae ya kwashe su yana kallonta yace "takalman waye wnn" da sauri fuskarta daure tace "na wa" wani irin kallo ya shiga mata lkci daya yana bin falon da kallo kmr me son gano abu, dawowa cikin falon taga yyi ya nufi sama, da gudu ta bi bayansa tana cewa "ina xaka" bae ko kalleta ba ya shiga haura stairs din, ta hau saman ita ma da gudu ta sha gabansa tana xaro ido tace "wae ina xaka" hankadeta yyi da karfi tayi baya xata fadi yyi saurin rikota kan ta kai kasa ta fado kansa, ba karamin tsorata tayi ba ta saka kuka, ya matsar da ita gefe xae wuce ta kuma shan gabansa cikin kuka tace "Allah sae ka fada min inda xa ka" a nutse yana kallonta yace "ina ruwanki," bae jira me xata ce ba ya kuma turata daga gabansa ya haura sama, dakinta taga ya bude ta fasa ihu ta kuma bin sa da gudu, da sauri ya shige dakin ya kulle ya shiga bin dakin da kallo a nutse, ido hudu suka yi da Meenah dake bayan kofar dakin kmr munafuka tana kallonsa, juyawa yyi yana kallonta da kyau yace "me ya kawo ki gidana" ta daure fuska tace "momy ce ta aiko ni gun fateema" wayarsa ta ga ya ciro, ko ba a gaya mata ba tasan momyn xae kira gashi bata ma san ta fito ba don bata gidan, da sauri tace "ni fa bbu Wanda ya aiko ni, na xo gaida fateema ne" Ashnaah ta shigo dakin tana hararansa tace "to meye don ta xo gidan nn, xaka wani...." Bata rufe baki ba taji saukan mari lafiyayye, ta dafe kuncin a gigice tana kallonsa, sum sum Meenah ta nufi kofa xata fita da sauri, ya fixgota yana mata mugun kallo snn ya shiga janta tana bin sa a baya har suka sauka downstairs, ita dae binsa kawae take bata ce komae ba don mugun tsoron Khaleel take tun da can, gate ya nufa da ita ya bude ya jefata waje, ya juya yana kallon mai gadi yace "don me xa ku dinga barin mun mutane na shigar min gida" mai gadin da tuni ya mike tsaye da ladabi yace "Ca tayi ita yar uwarka ce oga" cikin tsawa Khaleel yace "ta ina ta xama yar uwata? To daga yau kar ku sake barin ta ta shigo min gida, ban san ta ba" da sauri mai gadin yace "an gama oga" Meenah dake tsaye har lkcn wajen gate tana ma Khaleel wani matsiyacin kallo tace "Da yau ubana bae da gida ne xanyi kuka , amma ynzu kam sae dae inyi shewa, kana talaka da kai har ka isa ka gaya min gida, kasan waye ubana kuwa, u re decievin ur self with dis hel yhu cal home" tsaki ta ja tana masa wani matsiyacin kallo tace "nonsense" tana kai wa nn ta nufi titi abun ta da sauri da sauri, bin ta kawae Khaleel yyi da kallo, lkci daya ya saki murmushi yana gyada kai yace "xan yi maganin ki yarinya, sae kinyi da kin sanin sani na" kashedi ya kuma yi ma masu gadin kan kar su bari ta kuma shigo masa gida snn ya nufi balcony, xaune ya tarda Ashnaah a bakin stairs tana ta aikin rusa kuka har lkcn yana dafe da kuncinta, wani raxanannen tsawa ya daka mata yace "bar min falo na kar in taka ki" ganin bbu wasa tattare da shi yasa ta mike tana ci gaba da kukanta ta hararesa ta haura sama. Da daddare tana kwance daki taji an tura kofa ta juya tana kallon kofar ya shigo dakin rike da leda a hannunsa, kallo daya yyi mata ya ajiye ledan nn bakin kofar ya fice daga dakin, sae da ta ji ya shiga dakinsa snn ta sauko kasan dakin ta bude ledan taga abinci ne. [10/20, 11:32 PM] ‪+234 803 863 6764‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 52..... Washegari Ashnaah na jin fitar motar Khaleel da yamma ta fiddo wayar da Meenah ta siyo mata da sauri, tana hamdalan fitarsa a xuciyarta, don tun safe take jiran ya fita amma bata san me ya hanasa fita ba, takardar da ta rubuta nmbr dad din Zeenat da ta adana cikin Jakarta ta dauko ta kwashe a wayar snn tayi dialing, bbu bata lkci ya shiga, ta nufi gadonta tana murmushi ta xauna tana jiran a daga, amma har ya gama ring ba a daga ba, ta kuma kira nn ma ba a daga ba, bata wani damu ba don tasan ae xae ga miscals dole ya kira baya, nmbr mum dinta ta kira, bugu biyu ta daga, Ashnaah na murmushi tace "momyna," Momy ta amsa daga daya bangaren, Ashnaah ta gaisheta cike da jin ddin jin muryar mum dinta, kmr xata yi kuka tace "momy wae har ynxu Ashfah baxa ta xo ba" momy tace "xata xo mana, kar ki damu, da fatan dae kuna lfya" A dan sanyaye tace "lfya lau momy, Abba na fa" Momy tace "yana nn lfya" a hankali tace "momy xan iya kiransa ynxu" momy ta dan yi shiru snn tace "to ki kirasa" Ashnaah tace "to Bari in kirasa" a sanyaye ta katse kiran, snn tayi dialing nmbr dad dinta gabanta na faduwa ta kara a kunne, xuciyarta ya kusa shigewa cikinta jin yana ring, bugu uku ya daga tare da yin sallama, da kyar ta iya bude baki ta amsa sallaman muryarta na rawa, a hankali tace "ina yini Abba" "lfya lau" ya amsa a takaice, a sanyaye tace "Abba ni ce" yace "ke wa?" Kmr xata yi kuka tace "fateema ce Abba" bbu yabo bbu fallasa yace "kina lfya" nn da nn hawaye ya cika idonta ta shiga gyada masa kai kmr yana kallonta da kyar ta bude baki tace "eh Abba" yace "to madalla, ngd da gaisuwar" bae jira me xata ce ba ya katse kiran, Ashnaah ta fashe da kuka duk da taji ddin amsa mata ma da yyi, momynta ta kuma kira ta gaya mata ynda suka yi da Abbanta hawaye na bin kuncin ta, momy tace "to kiyi hkuri watarana Allah xae bayyana gskya, da fatan dae bbu wata matsala" Ashnaah tace "bbu momy amma ina son in xo gida, ki taya ni rokon Abba ya bar ni in xo don Allah" cikin kuka ta karashe mgnr, a sanyaye momyn tace "to xan masa mgna fateema, sae in gaya maki ynda muka yi, wnn layin ki ne" Ashnaah na goge hawayenta tace "ehh nawa ne momy anjima xan kira ki da daddare" a hka suka yi sallama da mum dinta ta shiga rusa kukan takaicin 'bata mata rayuwa da rabata da yan uwanta da Khaleel yyi, ko kadan bata ji shigowarsa gidan ba kawae ji tayi ya bude kofar ta, ta daga kai da sauri tana kallon kofar hawaye na bin kuncinta, kauda kanta tayi da sauri tana ci gaba da kukanta, tsayawa yyi bakin kofar yana kallonta, can ya karaso Cikin dakin ya tsaya gabanta fuskarsa daure yace "me ya faru?" Tsaki tayi ta mike a fusace ta nufi bathroom, ya fixgota ta fado jikinsa, ta fashe da wani matsanancin kukan ta shiga turasa da karfi, amma ya ki sakinta, don kanta ta gaji tayi lamo a jikinsa tana shesshekar kuka, ya dago kanta yana kallon fuskarta ta daga idanuwanta tana kallonsa, kasa cewa komae yyi, ta kauda kanta da sauri, sae a snn yace "kukan me kike" ta fashe da wani Sabon kukan tace "ni gidanmu xan tafi" da kmr baxae ce komae ba yana mata mugun kallo can dae yace "kije kiyi me" ta daga kai ta galla masa harara snn tace "mamata da yan uwana xan je in ga" tsaki ta ji yyi ya turata yace "u are dreamin" snn ya juya ya fice daga dakin. Har dare Ashnaah bata bar kukan da take ba wani mugun tsanar Khaleel kawae take har cikin xuciyarta, don kanta ta gaji da kukan wajajen Karfe goma, snn ta mike ta shiga bayi tayi wanka ta wanke baki ta fito, yar rigar baccinta riga da yar karamar Riga tasa bayan ta gama shafe shafenta snn ta dauki wayarta da ke karkashin filo tana mamakin me yasa Baban Zeenat bae kira ba bayan ta masa mis calls, ta kalli agogo ta ga is late, a xuciyarta tace "ae gobe xan kuma kiran ka" momynta ta kira bata daga ba tasan kila tana dakin Abba, har xata ajiye wayar sae ta tuna ummi, da sauri ta sa nmbrta ta kirata, bugu daya ummi ta daga Ashnaah tace "ke ni ce ykk, kun fara exams din ne" ummi tace "wllh saura sati biyu Ashnaah ynxu baxa ki rokesa ya bar ki ki dawo ba" Ashnaah da taji kmr ta sa kuka tace "wllh nasan baxae bar ni ba kona gaya masa wayyo Allah na" ummi tace "kai amma gskya bn ji ddi ba" Ashnaah tace "yauwa mum dinsa na so na, kila idan na mata magana xata ce ya bar ni don yana jin mgnr ta ssae" kmr xata yi kuka ta karashe mgnr, ummi tace "yauwa ki mata mgna" Ashnaah tace "to ngd xan mata" a sanyaye ta katse kiran ta kwanta tayi jigum, usman ta tuna, ta Mike xaune da sauri tayi dialing nmbrta ya shiga ring, wani irin ddi ta ji har cikin ran ta, jin ya daga yasa ta dafe kirjinta ta wara manyan idonta, da muryar sa me sanyi da ddin sauraro ta ji ya mata sallama, ta amsa murya can ciki idonta lumshe, sunanta taji ya kira da mugun mmki yace "Ashnaaah" ta bude ido da sauri tayi yar dariya tace "na'am ashe baka mance murya ta ba dear" Ya sauke ajiyar xuciya yace "don me xan mance muryar ki fateema, y? Meyasa kika min hka fateema?" Kmr xae yi kuka ya karashe mgnr, nan da nn idonta ya kawo ruwa muryar ta na rawa tace "nt my fault dear," kuka ta fashe masa da a hankali tace "kar ka damu dear ni taka ce I promise yhu dat" da kyar yace "kin fito ne Ashnaah" ta girgixa kai hawaye na bin kuncinta tace "aa, amma in Allah ya yrda na kusa fitowa very soon" a sanyaye yace "Allah yasa, ranan ma naje gaida momy" hira ssae suka shiga yi irin ta masoya, ita kanta tasan duk duniya bbu wnda take so irin usman, har kusan sha biyu waya suke, lkci daya taji an bude kofar dakinta, in da Allah ya taimaketa duk wutan dakin a kashe suke, ta kashe wayan da sauri gaba daya ta tura karkashin filo, ta rufe ido kmr me bacci gabanta na faduwa, kunna wutan dakin yyi yace "ke da wa naji kmr kuna mgna a nn" yi tayi kmr bacci take gabanta na faduwa, ya karaso kusa da gadon yana kallonta, a hnkli ya duka dab da ita yana kallon kirjinta da kusan rabinsa duk a waje yake, kan dogayen kafafuwanta ya kuma sauke ido don iyakar wandon gwiwa, wani kasala ne ya dirar masa nn take, ya hadiye miyau da kyar yana kallon fuskarta, ita kam bnda bugawa bbu abinda xuciyarta ke yi, mikewa yyi da kyar kmr Wanda ya sha wani abu ya nufi gun switch din dakin ya kashe snn ya dawo gadon, a tsorace Ashnaah ta mike xaune [10/20, 11:54 PM] ‪+234 803 863 6764‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 53..... Bata bari ya karaso kusa da gadon ba ta Mike da sauri xata sauka ya fixgota da karfi ta fado jikinsa suka fada kan gadon, kuka ta saki jikinta na rawa hka ma muryarta tace "don girman Allah kayi..." Toshe mata baki yyi da hannunsa, ya kankameta yana kissing wuyarta, cikin wata kasalalliyar murya kmr wani mashayi taji yace "hakki na xa ki bani yau, ko ban maki kokari ba?" Ashnaah ta xaro ido kmr yana ganinta ta fashe da wani matsanancin kuka tace "wayyo na shiga uku, wllh ni ban gane me kke..." Bakinsa ta ji cikin nata lkci daya ta ji yana mata wasu abubuwa da suka kusan sumar da ita don tsoro, bbu abinda ya kuma raxana ta irin ynda ta ji yana kkirin cire yar rigar jikinta, ta rike rigar gam muryar ta na rawa jikinta na bari ta shiga cewa "kayi ma Allah ka rufa min asiri wllh ni yarinya ce, me xaka min" ko kadan bae ma san tana yi ba, kmr Mara hnkli kawae ya xaman Mata, ya rabata da rigar jikinta da karfi, ta fasa wani ihu a tsorace, ya toshe bakinta da sauri yana mayar da numfashi, bbu inda baya rawa jikinta don tsoro, duk kokuwan da ta dinga yi da shi hkn bae hanasa rabata da komae na jikinta ba don karfi ya gwada mata, nn da nn tayi laushi ta rungumosa cikin kuka ssae take cewa "plss doctor ka tausayamin wllh baxan iya ba plss" Khaleel bae ma san tana yi ba, ita dae daga nn bata kuma sanin abinda ya faru ba don sume masa tayi. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 54...... Khaleel ya mike xaune da kyar yana kallonta da idanunsa da suka sauya kala ya dago ta ya rungumeta tsam yana mayar da numfashi, sae da ya dan ji nml snn ya kwantar da ita a hnkli ya mike ya nufi bathroom dinta. A hankali Ashnaah ta bude idonta da ya kumbura don kuka da asuba, kasa tuna abinda ya faru tayi ga wani mugun ciwo da kanta ke mata, bin ko ina ta shiga yi da kallo kmr me son tunano abu, lkci daya kuma ta tuna abinda ya faru jiya, da sauri kuma a gigice ta mike xaune ta sauko daga kan gadon ta fashe da kuka tana bin ko ina na jikinta da kallo a tsorace, bata ga alaman komae ba ga kayan baccin ta kuma a jikinta, maida Dubanta tayi kan gado nn ma bata ga komae ba, duk da hka ba ta fasa kukan da take ba, bude kofar dakinta taji anyi ta juya da sauri tana kallon kofar, yana tsaye ya harde hannayensa a bakin kofa yana kallonta, kauda kanta tayi da sauri tana ci gaba da kukanta, ya karaso cikin dakin, tana ganin hka ta nufi bathroom da sauri ya rikota ya juyo da ita yana kallon fuskarta, kin bari su hada ido tayi sae kuka take, murya can kasa yace "u feigned false faintin jiya don kar ki bani hakki na ko?" Kauda kanta tayi lkci daya ta daure fuska, yyi mumushi yana shafa sajensa yace "nasan maganin ki ae" ita dae bata ce komae ba ta wani hade rae sae dae gabanta faduwa yake, hannunsa ta ga ya daura a kirjinta yana mata wani irin kallo ta buge hannunsa a dan tsorace, yyi wani irin murmushi yana kallon kyakkyawan Fuskarta yace "very soon, xan baki matsayin xama mistress dina, don in dinga hutawa da ke naga alamar xa ki yi ni'ima ssae, ke ma kuma taimakon ki xanyi" a fusace ta turasa ganin yana neman rungumota, muryar ta na rawa tace "ni ba mistress din ka bace wllh na fi karfin xama hka" dariya yyi yana kallonta da mmki yace "ohh hka kika ce ko, to Allah ya kai mu nyt, bby ba suma ba, ko fixge fixgen mutuwa kike wllh sae na....." Ihu ta fasa don bata ma son jin abinda xae ce, jikinta ba kwari ta durkushe wajen ta fashe da wani matsanancin kuka tana girgixa kanta tace "wllh Allah ya fi ka, bbu abinda ka isa ka min, Allah baxae taba Baka iko ba, in' sha Allahu da budurcina xaka rabu dani kmr ynda ka sameni, don kai ka cuceni ni ban cuce ka ba, mugu kawae axxalumi wllh baka isa ka min komae ba virginity dina ba naka bne..." Kasa ci gaba da mgnr tayi kuka ya ci karfinta ssae, yyi murmushi xuciyarsa na tafarfasa yana gyada kai yace "xa ki yi bayani ltr" juyawa yyi ya fice daga dakin. Hka Ashnaah ta wuni ranan kuka, har yamma tana nn inda ya bar ta sllh kadae ke tada ta, da tayi kuma xata dawo ta ci gaba da kukanta daga inda ta tsaya duk abun duniya ya isheta, bbu abinda ke daga mata hnkli irin ynda taji yace xata yi bayani, ba karamin tsoratata yyi jiya ba hkn yasa hnklinta yaki kwanciya, gani tayi yunwa na neman yi mata illa ta mike da kyar ta nufi bayi ta wanke bakinta snn ta fito ta sauko downstairs wajajen Karfe biyar, indomie ta dafa snn ta hada tea ta koma sama, ta shiga tura abincin da kyar don bata da appetite ko kadan. Biyar da kusan rabi khaleel ya gama clearing office dinsa yana durkushe kusa da show glass din magungunan dake office dinsa yana xaban wasu magani Najeeb ya shigo yana cewa "yhu re still around" boye maganin hannunsa Khaleel yyi da sauri, Najeeb ya karasa kan table din office din yana kallon tablets din da ke kai guda daya, mikewa Khaleel yyi da sauri don ya manta ya ajiye daya a kan table, da mmki Najeeb ya juya yana kallonsa yace "me xaka yi da wnn Khaleel" Khaleel yyi kmr bae ji sa ba, ya karaso ya karbe maganin a hannunsa ya bude briefcase dinsa ya saka a ciki, najeeb ya kuma yi masa tambayar, kallonsa Khaleel yyi yace "wani xan bae ma" Najeeb ya girgixa kai yace "no, say d truth pls" khaleel yyi masa mugun kallo yace "da'alla ka rabu dani Najeeb" Najeeb yace "no! don Allah Khaleel ka kyale yarinyar nn, she is too young plss, injury ssae xaka mata ba kadan ba in kayi amfani da tablet din nn, plss leave her 4 now, kae da xaka yi aure ma nn da sati biyu, don Allah kayi hkuri ka bar ta ga Ameeshan ka" da damuwa ssae Najeeb yyi mgnr, har hkn ya ba Khaleel mmki, tsaki yyi ya dauki briefcase dinsa yace "ka ga fito xan kulle office Dina" bae jira me xae ce ba ya nufi kofa Najeeb ya bi sa a baya yana cewa "ynxu baxa ka saurare ni ba Khaleel" sae da Khaleel ya kulle office dinsa snn yana kallon Najeeb yace "yau kuma kai ke cewa in kyaleta, amma abun da mmki, can't blve it" yana kai wa nn yyi gaba ya bar sa nn tsaye. Najeeb ya bi sa da sauri yace "ae sae da naje ranan na ga ashe yarinya ce ssae shi yasa ka ga hka, plss frnd gwara ka saketa kar ka lalatata she is 2 young" shakesa Khaleel yyi yana huci yace "kae baka isa ka gaya min ynda xan yi da matata ba, ina ruwan ka da iyali na, kama san abinda tayi min daxu ne, so just hold on, in kaga na kyale yarinyar nn yau ko.." Wani irin murmushi yyi yana girgixa kai snn ya nufi motarsa da sauri ya bar Najeeb nn a tsaye. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 55..... Ashnaah na kwance dakinta wajajen Karfe tara ta ji shigowar Khaleel gidan, mikewa xaune tayi a hnkli gabanta na faduwa, jiki ba kwari ta jingina jikin gadonta, tana ji ya hauro sama ya bude kofar falonsa ya shiga, ta hade kanta da gwiwa hawaye mai xafi ya shiga bin kuncinta, tana nn xaune har kusan Karfe goma sha daya, daga karshe ta mike da kyar ta nufi kofarta ta kulle da key snn ta nufi bathroom don yi wanka, ko da ta fito turare kawae ta shafa ta Dauki rigan baccinta ta saka snn ta daure gashinta ta sa net ta kashe wutan dakin ta nufi kan gadonta a hnkli ta kwanta tare da lumshe idonta, nn da nn bacci ya dauketa, can cikin bacci taji kmr saukan numfashi a wuyarta, ta farka a tsorace suka yi ido hudu da shi don ya kunna bedside light, kuma me haske ne ba laifi, kmr me jin bacci ta ga manyan idanuwansa, mikewa ta shiga kkrin yi da sauri xuciyarta na bugawa xata bar wajen, ya fixgota jikinsa, ta saka kuka da karfi "wayyo na shiga uku, don Allah ka rabu da ni plss, am begging..." Bakinsa ya cusa cikin nata, ta shiga dukansa da duk karfinta tana neman kwace kanta, ya fadar da ita kan gadon ya danneta da karfi, kasa ko da kwakkwaran motsin kirki tayi, abubuwan da suka fi wnda yake Mata da ya shiga mata ba sassauci, duk jikinta yyi sanyi ssae, ta kasa yin komae sae kukan da take tana rokonsa, tana ji lkci daya ya raba ta da komae na jikinta, ta fasa wani ihu a gigice muryarta na rawa ta daura hannu a shoulders dinsa tana girgixa masa kai hawaye na bin kuncinta tace "doctor no no, plsss I beg yhu kayi hkuri wllh baxan sake ba plss, wayyo na shiga uku, ka tausayamin don Allah" toshe bakinta yyi, ita kanta tasan Khaleel bae san tana yi ba don abun nasa sae ta ga ya fi na kullum, lkci daya wani karfi ya xo mata ta shiga kokuwa da shi tana neman kwace kanta, shaketa yyi yana kallon cikin idonta da idanuwansa dake bata tsoro, cikin wata kasalalliyar murya yace "its either ki tsaya ko kuma in maki ta karfi" wani kuka mai ban tausayi ta shiga yi ganin abinda yake shirin yi, ta kankamesa muryarta na rawa tace "wayyo pity me plss wllh baxan iya ba kar ka min hka" rasa dalilin da ya hanata suma kawae tayi a wnn lkcn don har wani daukewa numfashinta yake don tsoro, ba karamin wahala Ashnaah ta sha hannun Khaleel ba ranan don bbu irin jagwagwalatan da bae yi ba, amma ya samu kansa da kasa mata komai duk da ynda ya so yin hkn, ko don irin ynda yaga take kuka kmr xata shide ne shi kansa ya kasa ganewa, da kyar kmr wani Mara lfya ya mike ya fada bathroom din dakin, Ashnaah ta sauko daga kan gadon da sauri tana ci gaba da kuka har lkcn jikinta bae bar rawa ba, ta dauki zaninta ta daura jiki ba kwari ta nufi kofa amma ta ji shi a rufe, durkushe wa gun tayi ta hade kae da gwiwa tana rera kuka a hnkli, tana nn a hka har ya fito ya nufi kofa xae fice daga dakin, mikewa tayi da sauri xata bar gun tayi baya xata fadi yyi hanxarin rikota ta fado kansa, ba karamin tsora tata bugun kirjinsa yyi ba, ya dago kanta yana kallonta da idanunsa da suka yi ja ji da yyi jikinta yyi xafi don ko kadan bae lura da hkn ba suna kan gado, rufe fuskarta tayi a faffadan kirjinsa tana shesshekar kuka don bata son su hada ido, ya nufi kan gado da ita suka xauna har lkcn tana jikinsa, dago kanta yyi yana kallon idonta, ta sunkyar da kanta da sauri, murya can kasa yace "baki da lfya ne" kin dago kanta tayi ya mike ya fita daga dakin, a hnkli ta kwanta kan gadon tana ci gaba da kukanta, dawowa yyi dakin rike da tablets da ruwa a hannunsa ya bude ya ajiye ruwan snn ya dago ta ya mika mata, ba tare da ta kallesa ba ta karba ya dauki ruwan ya bata ta sa maganin a baki snn ta kora da ruwan, toshe bakinta tayi da sauri ya rikota tun kan ta mike yace "amae" gyada masa kai ta shiga yi da sauri, ya kwantar da ita jikinsa ya shiga shafa mata baya a hnkli, ta lumshe idonta, sun fi minti goma hka jin saukan numfashinta a hnkli a kirjinsa yasa ya gane tayi bacci, ya kwantar da ita snn ya Mike ya fice daga dakin. Washegari da asuba yana idar da sllh ya shigo dakinta, xaune ya sameta kan darduma ta dauke kanta da sauri, ya rungume hannayensa bbu yabo bbu fallasa yace "ya jikin" ita ma ba tare da ta kallesa ba tace "da sauki" juyawa yyi ya fice daga dakin, ta bi sa da harara ta mike ta koma kan gado tayi kwanciyarta nn da nn bacci ya kuma dauketa. Da yamma Ashnaah na xaune ita kadae a daki tayi jigum duk abin duniya ya isheta, kmr warce ta tuna abu sae kuma ta mike tsaye da sauri ta nufi gaban madubinta ta bude drawer ta ciro wayar da ta boye a ciki, kunna wayar tayi don tun ran da ta kashe da daddare bata kuma bin ta kan wayar ma, mum dinta ta shiga kira tana daga wa suka gaisa snn Ashnaah tace "momy kin yi ma Abbana mgna" momy tace "ehh na masa amma ki bari ran lahadi ki xo fateema" ddi ne ya kashe Ashnaah jin abinda mum dinta tace, sallama suka yi Ashnaah ta shiga tunanin ynda xata yi Khaleel ya bar ta ta je gida, tafi minti ashirin tana ta tunane daga bisanni ta sauke ajiyar xuciya ta shiga neman layin usman, bugu biyu ya daga, yace "haba Ashnaah don me kika kashe waya ranan without even sayn a gud bye," Ashnaah tace "oh ba laifi na bne wllh kayi hkuri" ya sauke ajiyar xuciya yace "kin bar ni da tunanin ki Ashnaah, na kasa mancewa da ke a rayuwata" Ashnaah tace "kar ka damu usman nayi maka alkawarin am urz only," a sanyaye yace "to Allah yasa, ynxu dae ba daman mu hadu knn koh" Ashnaah ta dan yi shiru snn tace "duk ran da na samu fita xan kira ka mu hadu don tun da na shigo gidan ban taba fita ni kadae ba" danna kararrawan da ta ji an yi yasa tayi masa sallama da sauri snn ta katse kiran ta sauka downstairs tana tunanin me kuma xata yi ma masu gadi da suke danna bell, don su kadae ke danna bell a gidan, tana bude kofar ta koma baya da sauri tana kallonsa, lkci daya ta shiga kkrin tuna inda ta taba ganinsa, ya sakar mata murmushi Mae kyau yace "kin gane ni" shiru tayi bata ce komae ba duk da ta ganesa a lkcn, yace "can I cum in" hanya ta basa ya shigo falon snn ta juya ta nufi cikin falon yana biye da ita a baya, tambayarta ya kuma yi ko ta gane sa, bbu yabo bbu fallasa tace "eh" yace "OK, came 2 help yhu fateema, ko baki bukatan taimako na" ta hade rae tace "wani taimakon xa ka min," yana kallonta yace "kina son ci gaba da xama da Khaleel a matsayin mijin ki knn" da sauri tace "aa, no wllh" yace "ok, in kin bni hadin kai Dari bisa Dari na maki alkawarin raba auren ku, don't think negatively don nace ki bni hadin kai am nt here 2 hurt yhu but to save yhu" mikewa yyi yana kallon agogon hannunsa yace "let me leave, I knw he is on his way now" da sauri Ashnaah tace "to xaka kuma dawowa ne" yace "idan Allah ya yrda but not soon" bae jira cewarta ba ya nufi kofa da sauri ya fice daga falon ta bisa da kallon mmki, to taya xae taya ta kashe auren yana abokinsa, wani mugun farin ciki ne ya xo mata tayi murmushi ssae ta nufi sama tunani kala kala na mata yawo a ka. 56..... Karfe shidda na yamma Khaleel ya tura kofar dakin Ashnaah, tana xaune bbu abinda take sae tunane tunane, fuskarsa a daure yace "in kin ga dama ki sakko kasa ki sameni" binsa da kallon tsana tayi har ya bar bakin kofar snn ta ja tsaki hade da tabe baki, mikewa tayi gudun kar ya dawo ta dauki hijab dinta tasa snn ta fesa turare ta sa takalminta ta sauka kasa, yana cikin mota yana jiranta, tana shiga ya ja motar suka bar gidan. Gidansu yyi parking ya fito ya nufi cikin gidan, ita ma ta fito tana biye da shi a baya, suna gama gaisawa da ummi Khaleel ya fita ya bar dakin, sae a snn ummi ta juya tana kallon Ashnaah tace "ya kawo maki kaya fateema" Ashnaah ta dan yi shiru snn tace "A'a" ummi ta tsaya kallonta, ta sunkuyar da kanta, ummi da tuni bacin rae ya bayyana fuskarta tace "kudi fa" girgixa mata kai Ashnaah tayi ba tare da ta dago ba alamar aa, ummi ta mike ta fice daga dakin, sae bayan kusan minti sha biyar ummi ta dawo, Khaleel ya shigo dakin yana kallon Ashnaah da mmki yace "ki ka ce ban kawo maki kaya ba ke" Ashnaah ta galla masa harara tace "ehh ni bn ga kaya ba" kallonta ya tsaya yi ya ma rasa me xae ce, ummi ta daka masa tsawa tace "dalla fice min a daki malam" juyawa yyi ya fice daga dakin, Ashnaah ta juya tana kallon ummi murya can kasa tace "momy don Allah ki taya ni yi masa mgna ya bar ni in ci gaba da karatuna, ni nayi masa ya ki yrda, kuma ya ki bari na in je gida har ynxu. Karfe goma saura suka bar gidan, gaban Ashnaah sae faduwa yake ganin ynda ya hade rae har suka isa gida bae ce komae ba ya nufi cikin gida ba tare da ya tsaya kulle motarsa ba, a sanyaye gabanta na ci gaba da faduwa ta bi sa, har ya shige falonsa kanta shigo falon, ta bude dakinta a hnkli ta shiga ko xama bata yi ba taji ya bude kofarsa ya fito, tayi still xuciyarta na bugawa, dakinta ya bude ya shigo ya nufi inda take fuskarsa daure ya fixgota yana huci yace "ki gaya min dalilin da yasa kike hada ni da ummi na" kuka ta saki tana kallonsa tace "to ni wani kaya ka bani don Allah" turata yyi da karfi yace "kuma da kike cewa xa ki koma makaranta uban wa xae dinga biya maki kudin makarantar, kin ban ajiya ne, in kin tafi gidan naku sae ki gaya ma mahaifin ki ke makaranta xa ki koma don baxan daura ma kaina wnn nauyin ba" juyawa yyi ya fice daga dakin, Ashnaah ta bi sa da kallo tana mmkin dukanta da bae yi ba, ssae jikinta yyi sanyi tuna furucinsa na karshe, to ynxu abbanta zae yadda ya ci gaba da biya mata kudin makaranta? A sanyaye ta nufi gadonta ta kwanta tana tunanin to ko dae usman xata yi ma mgna. Yau Sunday tana kwance daki taji an danna kararrawa, ta mike ta dauki hijab dinta ta sa snn ta sauka downstairs ta bude kofar, gaisheta mutumin yyi yace "oga ne yace xa a fita da ke anguwa yau" da mmki tace "ni? Ina yace xa ni?" Mutumin yace "cikin gari yace xa a kai ki" cike da murna tace to ka je ka dawo bari in shirya, da sauri ta koma sama, har wani bari jikinta yake ta shiga fiddo kayan da xa ta sa, ta fito da wani atamfanta England me kyau ta ajiye snn ta shiga gyara fuskarta don dama tayi wanka, ssae tayi kyau ba kadan ba, a karo na farko ta bude akwatunan lefenta ko xata ga jaka da takalmin da xae shiga da kayan don tana da mayafi, ta ko samu har ma da mayafi duk light yellow, ba karamin haduwa Ashnaah tayi ba, jan baki ya kwanta das das lebbenta me kyau, ita kanta tasan tayi ne, turarrukan da ke gaban madubinta ta feffeshe snn ta kuma kallon kanta a madubi ta fice daga dakin ta sauka kasa cike da jin ddin xata gidansu daga nn ma sae su hadu da usman dinta, xaune ta samu Khaleel a falon yana waya kallo daya yyi mata xae dauke kae ya kasa da sauri ya kuma juyawa yana kallonta, ko kallonsa bata yi ba har ta wuce sa xata fita ya daka mata wani mugun tsawa yace "ina kike tunanin xa ki da mayafi? Da aure na a kan ki xa ki shiga gari da wnn dan iskan mayafin" juyawa tayi tana hararansa tace "to me xan sa? Kana nufin in yaba hijab kan kwalliyar nn, tabdi lallai ma" mikewa yyi a fusace ya yo kanta ta jefar da heels din kafanta ta sa ihu ta nufi sama da gudu, bin ta yyi har cikin dakints ya fixge mayafin, hadiye kukan da ke cinta kawae take don kar ta bata fuskarta, da kansa ya ciro Mata hijab har kasa ya jefa mata snn ya fice daga dakin, bbu ynda ta iya hka ta sa hijab din kmr xata fashe da kuka ta fito, har waje Khaleel ya bi ta yana kallon drivern da ke jiran ta jikin mota yace "ba ni makullin motar Ahmad, xaka iya tafiyarka xan kai ta" Ashnaah ta juya da sauri tana kallonsa, ji tayi kmr ta fasa ihu, shi ko ya xagaya ya shiga maxaunin driver, dae dae lkcn da masu gadi suka bude gate sae ga babban mota dauke da lafiyayyun kayan daki na gani na fada, har su biyu suka shigo gidan, Bin motar da kallo Ashnaah tayi, Khaleel ya sauke glass din motar ya daka mata tsawa "wae kina hauka ne xaki bar ni xaune cikin mota" ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 57..... Ashnaah ta bude motar ta shiga har lkcn tana kallon motocin da suka shigo gidan da kaya with much interest, ko kifta ido bata yi, Khaleel ya ja motar bayan ta shiga suka bar gidan, sae a snn ta juya tana kallonsa tana murmushi hade da washe hakoranta, ganin taki daina kallonsa yasa yace "wae lfya kike kallona hka" kmr jira take ta fashe da dariya har da kyakyatawa tana kallonsa tace "na ga ka kusa xama ango ne ina taya ka murna," bae ko kalleta ba ya mayar da hnklinsa kan tukin da yake, tace "kayan amaryar ne aka shigo da ynxu knn?" Ya galla mata harara yace "wnn ba Matsalar ki bace" shiru tayi tana hararansa, can kuma tace "to yaushe ne bikin" nn ma bae tanka ta ba amma fuskarsa a daure yake, tace "to ya naga baka sauya kujerun falo ba da tv ko Akwae sauran tym ne" parkin taga yyi a fusace ya fixgota da shirin xabga mata mari, ta fasa ihu tare da rike hannyensa ta boye fuskarta jikinsa tana basa hkuri, kallonta ya tsaya yi ya kasa dukan nata har lkcn yana rike da ita, ta dago kanta a hnkli tana kallonsa kmr xata yi kuka tace "to don ina taya ka murna, da ina bakin ciki ae baxan dinga tambayarka ba hka, amma tunda baka so na daina" turata yyi ya ja motar suka bar wajen, ba ta kuma cewa komae ba ta hade rae ita ma, ganin tuki kawae yake yasa tace "to wae a ina kasan gidan namu ne da kke ta wani tuki," ba tare da ya kalleta ba yyi murmushi yace "fitsararrki da girman kae ya sa nasan gidan ku" juyawa tayi tana kallonsa bata dae ce komae ba, can dae ta dauke kai hade da tabe baki tace "to ka ji ddi" har kofar gidansu yyi parkin ta bude mota xata fita ya fixgota yana kallonta da kyau yace "kika kuskura kika fita xuwa ko ina ban yafe maki ba don ba da izini na kika yi hkn ba, gidan ku kadae na kawo ki," ya kalli wristwatch din hannunsa yace "dis is after eleven, xuwa Karfe biyu ki shirya xan xo daukar ki" yana kai wa nn ya turata, ta fice daga motar tana masa wani matsiyacin kallo tace "to kai kuma a suwa, ae wllh daga nn sae inda mai na ya kare, kuma ina jiran ka Karfe biyun in ga ko shigowa xaka yi ka jawo ni" tsaki tayi ta shige gate dinsu, ya bi ta da kallo yana murmushi yyi reverse ya bar anguwar, da fara'a Ashnaah ta gaisa da Mai gadinsu snn ta nufi falonsu gabanta na faduwa ganin motar Abbanta a parkn space, murya can ciki tayi sallama ta shiga falon gabanta yyi mugun faduwa ganinsa xaune yana kallon news, kallo daya yyi mata ta dauke kai, Ashnaah ta karasa inda yake jiki ba kwari ta durkushe kasa a sanyaye tana kallonsa tace "ina kwana Abba" ba tare da ya kalleta ba idonsa na kan tv yace "lfya lau" daga nn bae kuma cewa komae ba, rasa abin cewa tayi, hkn yasa ta sunkuyar da kanta, ta kusa minti biyar a gun, shi dae bae ce Mata komae ba, nn da nn Hawkeye ya cika idonta ta mike a sanyaye ta nufi sama gwiwanta a sace, tana shiga dakin momynta ta xube nn gabanta ta shiga rusa mata kuka, momy ta dago ta a rude tana tambayarta me ya faru, cikin kuka tace "momy Abbana bae kulani ba" a fusace momy tace "to sae me, kada Allah yasa ya kula ki din ae ba gun sa kika xo ba" da kyar Momy ta lallasheta tayi shiru tana ajiyar xuciya, momy tace "daga gida kike?" Ashnaah ta gyada mata kai alamar eh, momy tace "ke daya kika xo" Ashnaah ta share guntun hawayen fuskarta tace "Aa shi ya kawo ni, Momy Ashfah pa?" Momy tace "tana gidan inna" Ashnaah tace "tana xuwa sch har ynxu ko" momy tace "eh tana xuwa" nn da nn wani hawayen ya kuma taruwa idon Ashnaah, a sanyaye momy tace "ke har ynxu baki koma ba ko?" Hawaye ya shiga bin kuncinta tace "ya ki Bari na in koma momy, ranan nayi ma mum dinsa mgna ta taya ni masa mgna ya bar ni in koma makaranta, sae da muka dawo gida yace shi baxae iya biya min kudin makaranta ba sae dae in babana ne xae dinga biya min" momy tayi shiru tana kallonta snn tace " ki fada min gskya fateema, kin san mutumin nn ko baki san shi ba" Ashnaah tayi shiru don tasan in ta gaya ma momynta gskyar abinda yasa Khaleel ya aureta kila ita ma fita harkanta xata yi don sau tari xancen ta baya wuce ta bar walakanta samari don bata san xuciyar wani ba sanin halin Ashnaah knn wlknta mutane," Ashnaah ta girgixa kai a sanyaye tace "Momy ni ban san shi ba" momy tace "to Allah xae saka maki, kuma ki kwantar da hnklinki wataran in Allah ya yrda gskya xata bayyana, kuma duk ran da hkn ya faru ni na tabbata ko Baban ki baxae bari ki ci gaba da xama da mutumin nn ba bare ni" Ashnaah dae bata ce komae ba kanta a kasa, momy tace "to ki tafi gidan inna ku gaisa kar kuma ki Mata xancen komae don tana iya tasowa ynxu ta xo ta sami Abbanku ta kuma ja maki matsala, kawae ki nuna mata lfya kike xaune da mijin ki, Ashnaah ta dan yi shiru duk da tana son xuwa taga kakar tata da yar uwarta Ashfah, can ta dago tana kallon momynta tace " momy bae san xan je can ba ae, kums Ca yyi kar in je ko ina daga nn" sake baki Momy tayi tana kallonta, Ashnaah ta dauki wayar momyn tace "bari kawae in kira Ashfahn ta xo ta sameni." Like · 7 · Reply · Report · 12 minutes ago ~Dr Khaleel~ by Khaleesat Haiydar 58..... Karfe uku saura mai gadi ya danna bell, Abban Ashnaah da ke xaune falo har lkcn ya mike da kansa ya bude kofar, mai gadin ya gaishesa da ladabi snn yace "wae fateema ce mai gidanta ke jira a waje" Abba yace "OK bari ayi mata mgna" wayarsa ya dauka ya kira Ashfah da ke sama, nn da nn ta sauko tace "gani Abba" ya bata sakon mai gadin, ta koma sama ta shiga dakin Momynsu tana kallon Ashnaah tace "wae mijin ki na jiran ki a waje" Ashnaah ta hade rae tana hararanta, Momy tace "haduwa ku ka yi da shi ne" da sauri Ashfah tace "aa, Abba ne ya kirani ynxu yake gaya min, ina jin mai gadi aka aiko" momy ta juya tana kallon Ashnaah da tuni yanayinta ya canxa tace "to tashi ki tafi fateema, tun da Abban ku aka ba sakon" bata yi musu da momynta ba ta mike a sanyaye ta sa hijab, Momy ta bude Jakarta ta kirgo dubu ashirin ta mika mata tace "gashi sae ki rike a hannunki kiyi transport xuwa makaranta, kawae nuna masa xa kiyi Abbanki ne ya baki, kiyi ta hkuri wataran sae lbri kin ji" Ashnaah ta share hawayen da ke bin kuncinta, ta karbi kudin a hnkli tace "to ngd Momy, Allah ya saka da alkhairi" turarruka momy ta harhada mata snn suka rakota har Downstairs da Ashfah, Ashnaah ta karasa falon Abbanta a sanyaye ta duka tayi masa sallama, ya amsa tare da cewa "Allah shi kiyaye hanya" mikewa tayi tana kallon momynta da ke ta hararan mai gidan nata, ta dauke kai suka kuma sallama da momynta snn Ashfah ta rakata har bakin mota inda Khaleel ke jiranta a waje, daga inda take tsaye ta gaishesa murmushi dauke fuskarta, kallonta ya tsaya yi da mugun mmki, sae kuma juya yana kallon Ashnaah da ta hade rae har lkcn hawaye na idonta tana kallon Ashfah tace "nagode sister, ki gaida min da inna in kin je" Ashfah tayi murmushi ta daga mata hannu snn ta juya da sauri ta shige gida ganin ynda Khaleel ke kallonta har lkcn mmki bayyane a fuskarsa, juyawa yyi yana kallon Ashnaah a karo na biyu kmr xae yi mgna sae kuma ya fasa, tada motar yyi suka bar anguwar, idonsa na kan titi yace "dama ke twin ce?" Bnxa tayi masa Hkn yasa bae kuma cewa komae ba har suka isa wani babban shoppn mall. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 59..... Khaleel ya juya yana kallonta bayan ya gama parkn bbu yabo bbu fallasa yace "ki fita ki xabi abubuwan da kike so, sae kuma ki kuma xuwa ki ce ma ummina ban siya maki komae ba," yana kai wa nn ya fita, bbu musu ta fito ta bi bayansa suka shiga tayi shoppn dinta mai yawa, komae taga ni ko bae mata ba jefa shi cikin trolley take tsabar mugunta, shi dae bin ta da kallo kawae yake, har ta gaji don kanta fuskarta daure tana kallonsa tace "na gama." Yyi murmushi yace "tot baki gama muguntan ba ae" Kusan kayan dubu hamsin ta diba don yawancinsu duk turarruka masu tsada ne da takalma, ya biya kudin snn suka fito aka loda masu kayan a bayan mota, sae da ya fara siyan table water a gun da ake sayar da drinks cikin mall din snn ya nufi motarsa, Ashnaah ta juya tana kallon ruwan hannunsa ta hade rae tace "to ni ma Ae xan sha ruwan" juyawa yyi yana kallonta da kmr xae yi mgna sae kuma ya fasa, ya bude ruwan hannunsa ya sha kusan rabi snn ya rufe ba tare da ya kalleta ba ya mika mata, ta xaro ido tace "tab" ajiye ruwan sa yyi ya tada motar ys kama hanyar gida. Biyar saura suka isa gida, bata bi ta kan kayanta dake bayan mota ba ta nufi cikin gidan da sauri don xuwa ta ga gyaran da aka yi ma dakin amarya, mutane ssae ta tarar cikin gidan, duk suka bi ta da kallo, ita ma hka, tabe bak tayii ta nufi sama, dakin da ke kusa da nasa ake jeran, ta karasa bakin kofar dakin tana leken dakin ba karamin hadewa dakin yyi ba, kmr na wata yar shugaban kasa, ta tabe baki hadewa da cewa ikon Allah, kallonta kawae mutanen dake ciki suke da mmki, sae da ta gama kare ma ko ina kallo daga Bakin kofar snn ta juya xata bar wajen dae dae lkcn da Khaleel ya hauro sama, kallonta ya shiga yi yace "me kike yi a nn" a takaice tace "bai ma ido na abinci" bata jira cewarsa ba ta shige dakinta, sae da ta cire kayan jikinta snn ta dauki xani ta daura tayi kwanciyarta xuciyarta fess nn da nn bacci ya dauketa. Can after magrib ta farka tayi sllh, snn ta sauko downstairs sanye da hijab dinta, tsit kke jin gidan alamar duk an watse, falo ta tarar da Khaleel xaune yana cin fruit lkci daya yana waya, kallo daya tayi masa ta nufi kitchen tana tunanin me xata girka ta ci, daga karshe ta ga indomin ma baya ranta ta hada tea mai kauri ta fito, har ta nufi stairs sae kuma ta dawo tana kallon Khaleel fuskarta daure tace "gobe fa xan tafi sch" juyawa yyi yana Mata mugun kallo yace "get out ki ban waje" xaro ido tayi tana kallonsa ta ajiye tean hannunta da sauri ta xa gayo cikin falon tana kallonsa tace "ban gne ba, da xu nayi ma Abbana mgna, har ya ban kudin mota da xan fara xuwa, dama mun kusa fara exams in ji su ummi" yana mata mugun kallo yace "to bbu inda xa ki, bar min falona" kuka ta saki ssae tana cewa "wllh sae na je, tunda kace sae in ubana ne xae dinga biya min, kuma gashi ya bani kudin mota ya ce in tafi" mikewa yyi ya daka Mata tsawa yace "bar min falona kar in taka ki, Baban ki ke da iko da ke a ynxu ko ni, nace bbu inda xaki, kuma hkn ya xauna" kuka takaici ta kuma fashewa da ta rufe ido ta shiga fesa masa rashin kunya, ya yo kanta ta bar gun da gudu tayi ball da cup din tean da ta ajiye kasa, mug din ya tarwatse ruwan tean ya malale ta fasa ihu ta durkushe wajen, karasowa kusa da ita yyi da sauri ganin jini a kafarta, ya duka gabanta yace "subhanallahi" kuka ta dinga rusa masa tana yarfe hannu, ya Duba kafar ya ga yankewa kawae tayi a tafin kafar, daukar ta yyi ya nufi sama da ita ya bude falonsa ya shiga snn ya nufi bedroom dinsa ya xaunar da ita gefen gadonsa, cire mata hijab din jikinta yyi ganin har kasa yake ja, spirit ya dauko da cotton wool xae wanke mata gurin ta rike sa a tsorace tace "aa ni wllh bna so xafi xae min" ya ce "dan kadan xan sa maki, rufe idonta tayi lkci dayata ta saki ihu ta dafa kafadansa jin wani shegen xafi yana wanke wajen, daga kai yyi yana kallonta har lkcn yana rike da kafarta idonsa ya sauka kan kirjinta da yake hangowa daga durkushen da yake, bude ido tayi a hnkli tana kallonsa, ta xaro ido ganin abinda yake ta kare kirjinta da sauri, mikewa yyi shima da sauri ba tare da ya kalleta ba yace "jinin ya tsaya, nxt wk sae ki fara makarantar kafin nn an kawo min amaryata" mikewa tayi cike da jin ddi ta fice daga dakin. Ran Friday bayan an sauko daga juma'a aka daura auren Ameesha da Khaleel, Ashnaah kam ko a jikinta don ko momynta ma bata gaya ma ba bare wani nata, throughout ranan gidansu Khaleel ta yini da su Meenah don tun da safe ya kai ta, ummi tausayin Ashnaah kawae take don ta ga kmr yarinta yyi Mata yawa ganin ynda take ta harkan gabanta kmr ba kishiya aka mata ba, ita ko ranan dama ta samu dn sun fi awa biyu suna waya da usman dinta, bayan isha Ashnaah na kwance dakin Rukayya tana game da Sabon wayarta Meenah ta shigo rike da Jakarta alamar xata wuce, Meenah tace "wae fateema baki fada min ynda ku ka yi da Baban Zeenat ba ko daxu ta kirani wllh, ko dae har kin fara tausayin mijin naki ne" Ashnaah tace "wani tausayi? Ni wllh na ma manta, ae gwara da kika tuna min bari ma in je in kirasa ynxu wllh" Meenah tace "dare bae yi ba" Ashnaah tace Karfe fa takwas da rabi ynxu" mikewa ashnaah tayi ta fita don xuwa garden ta kira dad dn Zeenat, Meenah na biye da ita a baya. Dai dai bakin kofar fita suka hadu da Khaleel xa su shigo da su Najeeb, Meenah ta koma baya da sauri Khaleel ya shiga Mata wani irin kallo can yyi murmushi yana kallonsu Najeeb yace "nn da wata biyu xa ku kuma xuwa daurin aurena idan Allah ya yrda," Najeeb dae bae tanka sa ba sae kallon Ashnaah yake, juyawa Ashnaah tayi ta koma sama cike da jin haushin kiran da bata yi ba, Meenah ma ta ja tsaki ta bi bayanta. Karfe tara saura Khaleel ya sallami momynsa da ta ki sakar masa fuska tun da ya shigo gidan tafiya da Ashnaah, nasiha ssae ummi tayi ma Ashnaah kmr ynda xata ma yar ta snn tace ta tashi su tafi, Ashnaah ta mike tana kallon Khaleel shi ma ya mike snn yyi ma umminsa sae da safe ya fita. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 60..... Khaleel ya juya yana kallon Ashnaah bayan ya gama parkin yace "ina son maki wata tambaya" juyawa tayi tana kallonsa da mmki fuskarta daure tace "tambaya kuma" ya dan yi shiru snn yace "ki fada min gskya tsakanin ki da Allah, ke kika mare ni ko ba ke bace" dariya ma ya bata ssae, tana kallonsa da kyau tace "idan bani bace ba fa?" Bbu yabo bbu fallasa yace "yea sae in sake ki, in dauki revenge Dina kan warce ta marenin, I mean ur twin sis, don ni bana cuta, nd I wil ask for ur forgiveness of course" shiru Ashnaah tayi tana kallonsa, ba dan ba dan ba da tace ba ita bace but tana mugun son yar uwarta baxa ta so wani abu ya sameta ba, can tace "to idan bani ba ce fa?" Ya shafa sajensa yace "baxan sake ki ba har sae kin duka don kanki bayan na gama koya maki hnkli kina rokon in yafe maki kin gane kuskuren ki" Ashnaah tayi masa wani matsiyacin kallo snn ta fashe da dariya tace "dats d last thing da xan yi a rayuwa in duka ina baka hkuri don ni nasan ban maka komae ba kai ka min, ni da kai xa mu ga wnda xae gaji yyi surrender. Kuma karka kuskura ka sama yar uwata ido bbu ruwan ta ni ce nn Fateema na mare ka" Bata jira cewarsa ba ta fice daga motar ta nufi cikin gida, bin ta yyi da kallo snn yyi murmushi ya fito ya kulle motarsa ya bi bayanta. Ashnaah ta tsaya corridor din dakuna tana ta kallon dakin Ameesha tana tabe baki, dakin ta nufa ta tura kofar a hnkli tana kallon cikin dakin, xaune ta ganta kan rug din tsakar dakin ga kanwarta farida da kawayenta biyu xaune suna ta hira, da mmki Ashnaah ta ke kallon Ameesha don bata san ita ce amarya ba sae ynxu da take ganinta, Ameesha dae ta dukar da kanta, Ashnaah tayi murmushi tace "welcm to hell on earth yar uwa, har na tausaya maki wllh" juyawa tayi ta fice daga dakin, kawayen Ameesha da ransu ya baci suka ce wacece kuma wnn yar yarinyar ko ita ce uwar gidan, Ameesha bata ce masu komae ba sae hawayen da ta shiga yi, kanwarta Farida da baxa ta wuce Ashnaah ba tace "wat? Kuka kike ko me yaya? Wait wae ita kike ma kuka" a sanyaye Ameesha tace "nace ma Khaleel ya raba mana gida ya ki, ni bana son tashin hnkli wllh" farida ta fashe da dariya tace "wllh ba ki yo xuciyar mama ba Anty, ko ni na xage baxan ma yarinyar nn duka ba, dubeta kawae galallawa rai ba gata" dariya sauran kawayen Ameesha suka yi, Ameesha tace "ni dae bbu ruwana bana son tashin hnkli ki tashi ki tafi gida" farida tace "wllh bbu inda xa ni, in ta isa ta kuma shigo mana ta ga ko baxan ballata ba" Ameesha tamike a fusace ta nuna mata kofa tace "kinga tashi ki bar nn kar in bata maki rai" mikewa farida tayi ta fixgi Jakarta da yar mayafinta ta fice daga dakin, kawayen nata ma sun yi niyar kwana amma ganin abinda tayi ma yar uwarta yasa su ma suka mata sallama suka kara gaba, hkn yasa ta shiga kuka a hnkli ita kadae, a hka Khaleel ya shigo ya sameta, ya xauna gefen gado yana kallonta yace "wae kuka kike yi Khadija" bata ce masa komae ba hkn yasa ya mike ya fita ta bi sa da kallo a sanyaye. Bayan kusan minti talatin ya dawo dakin sanye da jallabiyarsa ya ajiye coffen hannunsa yana kallonta yace "kina ji na" ta dago tana kallonsa ya dan sakar mata murmushi snn yace "hope xa kiyi amfani da abubuwan da xan gaya maki" ta gyada masa kai kawae, yace "Kinga ke ce matata a gidan nn, don ita wancan she is just here for some tym, don hka duk wani responsibility na gidan nn na kan ki, tun daga kan girki nd every other chores, more importantly bbu ruwan ki da wancan yarinyar, ke ce matar gidan nn ba ita ba duk da nasan baki da fitina," yyi shiru snn yace "I think dats ol" ta sunkuyar da kanta tace "in sha Allah, I wil abide" daukan coffensa yyi ya karasa shanyewa, ita kuma ta mike ta nufi bathroom. Washegari da safe Ameesha na kitchen tana hada breakfst Ashnaah ta shigo kitchen din, ta tsaya daga bakin kofa tana kallonta, Ameesha ta dan yi murmushi tace "gud mrnin" Ashnaah tace "mrnin Amarya, girki kike?" Ba tare da Ameesha ta kalleta ba tace "ehh" Ashnaah ta karaso kitchen din ta dauki wata yar kula ta ajiye kusa da ita tace "to in kin gama ni ma ki xuba min nawa" tana kai wa nn ta juya ta fice daga kitchen din. Ameesha ta gama hada break din ta jera dinnin ta ajiye wnda ta xuba ma Ashnaah, dae dae nn aka bude kofar falon Farida ta shigo da kulan abinci, da mmki take kallon yayarta tace "wae girki kika yi" Ameesha tace "eh har na gama," farida ta tabe baki ta ajiye kulan hannun ta tace "sae anjima." Khaleel ya sauko downstairs yana kallon Ameesha yace "wa ya shigo ynxu" tace "farida ce ta kawo abinci" yace "OK" snn ya nufi dinnin ya xauna yana bude girkin da tayi, kulan da ta xuba ma Ashnaah ya bude yace "wnn fa" tace "Ca tayi in dibar Mata ita ma" wani kallo ya shiga yi mata yace "ita me ya hanata saukowa tayi" dae dae lkcn da Ashnaah ta sauko falon tana kallon Ameesha tace "har kin gama amarya" Ameesha tace "ehh ga shi can a dinnin na xuba maki" Ashnaah ta nufi dinnin din ba tare da ta kalli Khaleel ba xata dauki kulan ya Riga ta daukewa yana mata mugun kallo yace "ki shiga kitchen kiyi girkin mana" Ameesha ta karaso dinnin din tana murmushi tace "ae ta shigo taya ni daxu" ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 61.... Ashnaah ta gama feshe jikinta da turare snn ta saka hijab dinta ta dauki yar Jakarta ta rataye a kafada snn ta dauki dubu biyu cikin kudin da momynta ta bata ta fito, dakin Ameesha ta nufa ta sameta xaune gaban madubinta, Ashnaah tace "na tafi sch" da sauri Ameesha ta juya tana kallonta tace "da gske, ya bar ki ne" Ashnaah ta tabe baki tace "kar ma ya bar ni mana, kinsan ne xa ki girka mana yau" Ameesha tace "aa" Ashnaah tace "jollof rice" Ameesha tace "OK Allah ya kiyaye hanya amma ki fara gaya masa kan ki fita kar kiyi laifi" Ashnaah tayi dariya tace "ae ni bana laifi" juyawa tayi ta fice ta sauko kasa, xaune ta same shi falo, ba tare da ta kallesa ba ta nufi kofa, mikewa yyi da mmki yace "ina xa ki?" Ashnaah ta hade rae tana kallonsa tace "ba kace yau Monday Zan yi resuming ba" tsayawa kallonta yyi ya ma rasa me xae ce mata, can ya daka mata tsawa yace "to baxa ki ba, yar rainin wayo" kmr jira take ta fashe masa da kuka tace "amma kae fa kace min yau" yace "don nace maki yau shine xa ki xo ki wuce ni ba tare da kin ce xaki fita ba" ta dan marairaice gudun kar ya hanata tace "to nayi xaton bacci kke ae" tsayawa kallonta yyi ta sunkuyar da kai da sauri, ya kauda kansa yyi murmushi, can ya kuma kallonta yace "to a hka kike tunanin xa ki fita fuskarki a waje? Ina nikaf din ki" juyawa tayi ba musu ta koma ta sako nikaf snn ta sauko, daukar makullin motarsa da ke kan center table yyi fuskarsa daure yace "mu je" kmr xata fasa ihu take kallonsa don bata so ya kai ta ba, amma bata ce komae ba gudun kar yace bbu inda xata kuma, ta bi bayansa, har cikin makaranta Khaleel ya ajiyeta yana kallonta da kyau yace "na hane ki da yi ma ko wani namiji mgna, Karfe nawa xa ku gama lecture" tace "shidda" bata jira cewarsa ba ta bude mota ta fice. Ba karamin farin ciki su ummi suka yi ba ganin Ashnaah, ita kanta ta ji ddin ganinsu togeda once again, Karfe uku da rabi suka gama lecture dinsu na ranan, duk ta karbi handouts tayi foto copy don saura sati biyu exams dinsu, suna xaune karkashin wata bishiya gaba daya da kawayenta wajen shidda saura sae tambayarta ya mijinta suke ta ki basu amsa, mota suka ga yyi parkn dai dai inda suke, Ashnaah ta mike tana murmushi ta nufi motar, duk suka bude baki suna kallonta don tunda suka fito lecture ta kebe gefe guda tana waya basu kuma san da wnda take ba, bude motar tayi ta shiga, ya wara ido yana kallonta yace "waow my Ashhyy I missed yhu a lot " Ashnaah tayi murmushi tana kallonsa ita ma tace "same, sae da shidda ya kusa ka xo ko?" Yace "wllh daga xaria na taso sbda ke Ashnaah" tace "eyya to ya aiki ya kwana biyu" Yace "Alhmdllh dear, kin rame da yawa," murmushi tayi tace "ba dole ba" ya dan yi shiru snn yace "kin san bae dace mu xauna hka ba kina da aure Fateema, let move out mu samu ko karkashin tree ne mu xauna sae mu yi mgna" ta hade rae tana kallonsa tace "hka nace maka," yace "no dats d reality" Ashnaah tace "to na ji sae anjima" kiranta yyi a hnkli ta juyo tana kallonsa yace "ba mgnan fushi bne wnn its d fact," Ashnaah ta sakar masa kuka tace "ni ban san ynda xanyi ya sake ni ba, bana son shi, na tsanesa ya cuce ni, ya raba ni da kowa nawa" kuka ssae ta shiga yi, usman yyi shiru ya rasa abun cewa, can yace "to ina kika san shi Ashnaah" bata boye masa komae ba ta fada masa abun da ya faru tun daga farko har karshe, usman ya kasa daina kallonta da mmki, a hnkli yace "to ynxu ya kike so ayi" xata yi mgna ta hango motar Khaleel, cak komae na ta ya tsaya ganin dan nesa da su yyi parkin, tana kallon usman tace "na shiga uku gashi can ya xo" juyawa yyi yana kallon motar Khaleel, a tsorace Ashnaah tace "kasan me ka dan koma ta can sae in fito" bbu musu yyi ynda tace masa, ta bude Jakarta ta ciro nikaf da sauri ta sa snn tace "sae mun yi waya" ya gyada mata kai ta bude motar ta fice kmr munafuka. Da sauri da sauri ta isa gun da motar Khaleel yake tun daga nesa ya hangota ya kafa mata ido, tana iso wa ya hade rae yace "Daga ina kke" ita ma ta hade rae tace "cafe mana, na je foto copy" fito masa da handouts din Jakarta tayi da sauri tana nuna masa, bae ce komae ba ta xaga ta bude motar ta shiga ya tada suka bar wajen. Karfe takwas da rabi Khaleel ya shigo gida daga masallaci, Ashnaah na xaune falo da Ameesha suna kallo suna cin abinci, kallon abincin Khaleel ke yi yana yatsine fuska yace "meye wnn" Ameesha tace "jollof rice ne" yyi mata wani mugun kallo yace "kin ga ina cin sa ne da xaki girka," ta dan yi shiru snn tace "Ca tayi muyi jollof ne shi yasa nayi" Tsawa Khaleel ya daka mata yace "ita wa? Ita ta ajiye ki ko ni" Ameesha tayi shiru, Ashnaah ta mike hade da yin tsaki ta nufi sama da plate din abincin ta kmr xata tashi sama, masifa Khaleel ya shiga ma Ameesha kmr xae maketa ita dae bata ce komae ba har don kansa ya gaji yyi shiru ya nufi sama, sae a snn Ameesha ta fashe da kuka Ashnaah ta sauko a fusace tana kallonta tace "sae ki xauna takaicin namiji ya kashe ki, shi din wa da xae tsaya yana maki ihu kmr wani ubanki, iyye? idan ya maki ba kya iya ramawa sae da ki tsaya kiyi ta kuka, to wllh xa ki sha wahala, hka kawae ya maida ki kmr baiwarsa kullum cikin masifa, to wllh gwara ki canxa halin ki in xa ki ji ta nawa idan ba hka ba kina da wahala, kuma ko gobe abinda ran mu ke so a gidan nn xa mu girka, da da bae auro ki ba wani ke masa girkin ba eatry yake xuwa ba, to ynxun ma sae ya koma can" ynda kasan wata uwa da 'yar ta hka Ashnaah ta sa Ameesha a gaba tana mata fada, Khaleel da tun saukowar Ashnaah shi ma ya fito ya tsaya daga stairs yana kallonta yana murmushin courage dinta. ​Dr Khaleel​ By Khaleesat Haiydar 62 ..... Ashnaah ta juya a fusace ta nufi sama fuskarta daure bayan ta gama da Ameesha, bin ta da kallo Khaleel yyi har ta raba ta gefensa xata wuce ya fixgota ta fado kansa, duk da irin mugun tsoratar da tayi bata nuna ba ta dake tace "A'h meye hka" jan ta yyi ya nufi falonsa da ita ya kulle da key, sae a snn ta marairaice xata fara basa hkuri ya ja ta xuwa bedroom nn ma kulle da key, kuka ta saki tace "ni fa wllh ban san kana wajen ba shi yasa nayi mgna kayi hkuri" jinginar da ita yyi a Jikin bango ta ynda tana iya jiyo numfashinsa yana mata wani irin kallo yace "maimaimaita abubuwan da kika ce daxu, hkn kadae ne xae cece ki ynxu" Ashnaah tayi shiru a tsorace snn tace "me ma nace? OK kawae dae ca nayi ta daina barin kana mata ihu kmr ubanta," ta dan yi shiru kmr me naxari snn tace "sae kuma nace abincin da ke ranmu xa mu girka mu ci baka isa ka hanamu ba" kallon cikin idonta kawae Khaleel ke yi, ta kuma yin shiru tana tunani, sae kuma da sauri tace "nace kuma kar ta raga maka in kae mata ta rama" kmr xata yi kuka ta karashe mgnr snn a hnkli tace "shknn" kallon cikin idonta kawae Khaleel yake har lkcn, hkn yasa ta sunkuyar da kanta da sauri, ganin bae ce komae ba yasa ta dago kae tana kallonsa, lumshe ido ta ga yyi ya hade goshinta da nasa ya xagaye kugunta da hannunsa daya, bata ankara ba sae jin bakinsa cikin nata tayi, ta xaro ido a tsorace ta shiga tura sa tana kkrin kuka, rungumota yyi gam jikinsa ya shiga kissin dinta a hnkli yana mata wasu abubuwa masu rikitarwa lkci daya, duk ynda ta so kwace kanta kasawa tayi nn da nn jikinta yyi sanyi, hkn yasa ta sulale kasa ya bita, da yake ba ta karfi yyi mata ba kmr ynda ya saba ko da yaushe nan da nn ya kashe mata jiki, ssae Khaleel ya shiga romancing dinta ranan, na fitan hnkli kuma, ita kam bbu bakin mgna ina ma ta gan shi a lkcn, don kansa ya kyaleta ya mike ya shige bayi, sae a snn ta Bude idonta a hnkli ta gan ta kan gado, mikewa xaune tayi da sauri tana kallon jikinta ta jawo xaninta ta rufe jikin, sae kuma ta saka kuka ta sauka daga kan gadon da sauri ta nufi kofa xata fita ta ji shi a rufe, ta rasa ynda xata yi, ji take kmr ta nutse kan ya fito, hijab dinta tayi sauri dauka a kasa ta saka snn ta xauna kasan dakin ta hade kae da gwiwa ta shiga rera kukan jin haushin kanta, wanka Khaleel yyi ya fito bae ko kalleta ba ya saka sleeping robe dinsa ya kashe wutan dakin ya bar dim light snn yyi kwanciyarsa, Ashnaah ta dde xaune dakin har ta fara gyangyadi don kanta ta gaji ta kwanta kasan tiles din dakin, baccin minti talatin tayi sanyin tiles ya isheta ga kamshin hadari tana ji, mikewa tayi a hnkli ta nufi kan gado ta kwanta can nesa da shi nn da nn bacci ya kuma dauketa, can cikin dare ta farka ana ruwa ssae ta ji ta a jikinsa ya rungumeta bbu hijab din da tasa, dago kae tayi tana kallon kyakkyawan fuskarsa da curve din lips dinsa Mae kyau ga lips din ja, ta mayar da dubanta kan long lashes dinsa kmr na mace, ta kalli sajen fuskarsa da suka yi mugun kara masa kyau, a hnkli ta sauke idonta kan faffadan kirjinsa da ke bude ga ... read more Dr khaleel~ By Khaleesat Haiydar 63.... Takwas saura yan mintina Ashnaah ta gama shirinta na sch, a hanxarce ta sakko falo hannunta rike da nikaf da jakarta, goge goge ta samu Ameesha na yi a falon, ta nufi dinnin ba tare da ta kalleta ba Don zuwa ta ga me ta Hada na break, bbu komae kan dinnin din, hkn yasa ta nufi kitchen nn ma bata ga komae ba kitchen din Fes, falo ta dawo tana kallon Ameeshan tace "to ina breakfast dina, ba na ji kina girki ba daxu" ba tare da Ameesha ta kalleta ba tace na kai masa can daki, Ashnaah ta hade rae race "to ni sae in ci me" Ameesha xata yi mgna khaleel ya sauko rike da briefcase dinsa yyi shirin fita office yana kallon Ameesha yace "ki tafi ki kwashe abinda kika kai daki, a office xan yi break" Ashnaah ta nufi sama da Sauri sae ga ta ta sauko da flask da kayan tean da dan soye soyen da Ameesha tayi masa ta xauna nan tsakiyar falon ta shiga hada tean da Sauri, kallon ta kawae khaleel yake ya hade rae yace "da baki San xa kiyi break ba sae ynxu da xan fita, wllh kika bari na wuce bbu makarantar da xa ki yau" da Sauri Ashnaah ta shiga yin break din, yana tsaye yana kallon ta har ta gama snn ta mike da Sauri ta sa nikaf dinta ta hade rae tana kallonsa tace "na gama" Ba tare da ya kalli Ameesha ba yace "sae na dawo" a sanyaye ta amsa masa da Allah ya kiyaye hanya, ya fice daga falon Ashnaah na biye da shi a baya, har ta fita ta leko tana kallon Ameesha tace "yau ma kiyi mana jollof" Ana lecture Ashnaah ta rufe takardan gabanta da Sauri tana kallon Ummi da ke gefenta tace "ina zuwa" ummi tace "ina za ki" Ashnaah ba ta tanka ta ba ta fice daga class da Sauri, yana xaune inda yace mata yana jiranta, ta karaso tana murmushi tace "Welcm" shima yayi murmushin yace "thank yhu, ya lecture, hope ban yi interrupting din ki ba" ta yatsine fuska tace "ae an ma kusa gamawa" Usman yace "muna mgna jiya mijin ki ya zo" Ashnaah bata ce komae ba hkn yasa yace "to ya kike son ayi Ashnaah" ta dan yi shiru snn a hnkli tace "ni kawae so nake ya sake ni" Usman ya kafa mata ido snn yace "kin ban go ahead inyi duk abinda naga ya dace" Ashnaah tayi shiru tana kallonsa snn tace "kmr me knn" Usman yace "ke dae ki ban go ahead kawae" a hnkli tana girgixa masa kai tace "ni dae kar ka masa komae, kawae so nake mu rabu lfya" Usman yayi yar dariya yace "ae ni dama bbu abinda xan masa, kawae dae ki bani dama" Murya can kasa tace "to na baka" yyi murmushi yace "yauwa Ashyynah, just give me a wk" Ashnaah ta kirkiro murmushi bata ce komae ba, hira suka dinga yi har su ummi suka fito daga lecture, ummi ta tsaya da mmki tana kallon Ashnaah baki bude da sauran kawayenta, hkn yasa Ashnaah ta mike da Sauri tace "ka ga sae mun hadu gobe dear, ga malamae can sun kafa min ido kan a fara min wa'azi" khaleel na xaune office Najeeb ya shigo yana kallonsa da kyau yace "hope xa ka birthday din Maska gobe" khaleel ba tare da ya kallesa ba yace "nop" Najeeb yyi shiru yana kallonsa yana tunanin ta inda xae fara convincing dinsa ya je kar ya ruguxa masa plan, can ya sauke ajiyar zuciya ya xauna yana kallonsa yace "sbda me toh" ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 64..... Khaleel ya dago kai yana kallonsa yace "hka nn kawae me xan je in yi kmr wani mara aikin yi" Najeeb yace "ohh six months bck da kayi birthday dinka baka da aikin yi ne ko?" Khaleel yyi murmushi yace "bani da iyali ne a lkcn, da ina da baxan yi ba" Najeeb yace "cum on, kar kayi mana fuck up guy, kasan Maska won't be happy, ynda kuke da shi kace baxa ka birthday nasa ba is nt fair" Khaleel yyi tsaki ya ci gaba da abinda yake yace "ina ga kai gama aikin da ke gaban ka Yau shi yasa kke interruptn dina" Najeeb ya mike ya fice daga office din yana tunanin ta inda xae ja ra'ayin Khaleel su je birthday din abokin nasu. Karfe takwas da rabi Khaleel ya shigo gida, Ameesha da ke kitchen tana wanke wanke ta fito tayi masa sannu da xuwa xata karbi briefcase din hannunsa yace "don't bother je ki ki ci gaba da abinda kike" sama ya nufa har xae shiga dakinsa sae kuma ya nufi dakin Ashnaah tana kwance tana Duba handout din Chem, kallo daya tayi masa ta mayar da idonta kan abun hannunta, juyawa yyi ya rufe mata kofar ya nufi dakinsa, kasa bacci Ashnaah tayi ranan sae tunanin ynda usman xae yi ya sa Khaleel ya saketa take, ita dae ta ga ynda xa ayi wnn abun. Washegari da safe Khaleel ya xaune dinnin Ashnaah ta sauko da shirin sch, ta nufi dinnin din ta hade fuska tace "na shirya" wani mugun kallo yyi mata yace "kin ma raina ma kanki hnkli yarinyar nn, shi lecture din kullum ake yi da safe" hararansa ta shiga yi tace "da baka sani ba" yace "to bbu inda xa ki yau har sae kin kawo min timetable din ki" da sauri ta bude jakar hannunta ta fiddo timetable din ta ajiye masa gabansa, dauka yyi yana kallo, can ya ajiye ya ci gaba da shan tean gabansa, juyawa tayi ta koma falo ta xauna. Ameesha ta fito daga kitchen din ta nufi dinnin ta ja kujera ta xauna tana kallon Khaleel, daga kai yyi yana kallonta yace "lfya?" Ta dan yi murmushi tace "dama ina son ka bar ni in koma aiki ne plss" ajiye cup din hannunsa yyi ya hade rae yace "amma baki da hnkli, keep dis at d bck of ur mind dat as far as u remain in dis house bbu aikin da xa kiyi, Kinga nayi kama da irin maxa masu barin matansu su yi aiki" hawaye ne ya ciko idonta, ya Mike ya dauki wayoyinsa ya bar dinnin din, Ashnaah da ke xaune falo tayi dariya ta mike tana kallon Ameesha tace "sae kuma kika yi shiru kmr wnda aka dinke ma baki" juyawa tayi ta fice daga falon Khaleel ya bi ta da kallo. Khaleel na haraban hsptl yana xaune da wani patient dinsa suna hira najeeb ya karaso shima ya jawo kujera ya xauna bayan sun gaisa da patient din, patient din ya Mike yyi ma Khaleel sallama ya nufi cikin hsptl, Najeeb yace "Maska ya daga birthdayn sa sbda Kai, I told him u re very busy dis wk ba lallai ne ka samu xuwa ba, nd he decided to let it b on Sunday kaga wk end knn don hka baka isa kace baxa ka ba wllh" yau Sunday Ashnaah ta sauko falo rike da bucket dauke da hijjabanta da ta wanke a bayinta, Khaleel ya juya yana kallonta yace "ina xa ki" tace "shanya xan yi mana" ya mike da sauri yana kuma kallon dan ves din jikinta yace "a hka xa ki fita" ta hade rae tace "to su waye a gidan" wani tsawa ya daka mata ya nufi inda take ta ajiye bucket din da sauri ta bar gun tun kan ya iso tana hararansa, daukar bucket din yyi ya fice daga falon, Ameesha dae na kitchen tana lunch, yana fita da kmr minti biyar aka bude kofar wata mata ta shigo falon da sallama, Ameesha ta fito da sauri daga kitchen ta rungumeta cike da murnan ganinta suka karaso cikin falon, Ashnaah dae sae kallon matar take ko ba a gaya mata ba ta ga alamar uwar Ameesha ce, Matar tace "me kike yi a kitchen" dae dae nn Khaleel ya shigo falon rike da bucket, da mmki yake kallonta yace "Mama ke ce a gidan namu sannu da xuwa" a takaice ta amsa masa ya karaso cikin falon ya gaisheta da ladabi ta amsa bbu yabo bbu fallasa, Ameesha ta juya tana kallon Ashnaah tace "mum dita knn" Ashnaah tace "ae na ga alama ina yini mama" kin amsawa hajiyar tayi, Khaleel ya Mike ya nufi stairs ya ajiye mata bucket dinta snn ya haura Sama. Ashnaah ta tabe baki tace "ikon Allah" juyawa tayi ita ma ta nufi sama, hajiya ta mike tana kallon Ameesha fuskarta a daure tace "mu tafi daki" mikewa tayi suka nufi sama xuwa dakinta, Ameesha tayi shiru tana sauraron irin hudubar da uwar tata ke mata tana digestn, har ta Kai aya snn ta xuge Jakarta ta fiddo wani abu kulle a fallen xani ta hade rae tace "saura kuma don ubanki ki ki yi" Ameesha ta marairaice tace "amma fa ni momy tsoro nake ji" ta ja kunne ta da karfi tana huci tace "don ubanki ki xauna takaicin namiji da matarsa ya kashe ki tunda ke kince yar wahala ce," Ameesha tayi shiru tana kuma nazarin abubuwan da mum dinta ta gaya mata, kuma fa hka ne kila Ashnaahn ma ba xaune take ba don tana mmkin ynda duk irin tsiwan da take na Khaleel baya Mata komae sae dae yyi ta kallonta batun kuma yace mata baya sonta. Karfe biyar na yamma hajiya ta bar gidan, Khaleel na jin fitar ta ya shigo dakin Ameesha yana Mata mugun kallo yace "bna toleratin wnn a gidana in ganin juna kuke son yi to ki dinga shiryawa kina xuwa can gidanku kina samunta," hade rae Ameesha tayi bata ce komae ba har ya juya ya fice daga dakin ta dan yi murmushi a xuciyarta tace xaka gane kuranka. Karfe shidda da yan mintuna Khaleel ya shirya cikin nml dressing dinsa na 3qtre da farar polo ganin ynda abokansa ke ta damunsa da kira, ko kadan bae son ko wannensu ya xo gidansa shi yasa yyi deciding ya tafi kawae, ya fito dakinsa rike da car key dinsa har xae sauka sae kuma ya kuma juyawa ya nufi dakin Ashnaah, bacci ya sameta tana yi, durkushewa gabanta yyi yana kallon fuskarta ya daura hannu a hnkli kan shafaffen cikinta ta bude ido da sauri yyi saurin cire hannunsa ya mike tsaye, mikewa xaune tayi tace "meye hka" juyawa yyi ya fice daga dakin ta bi sa da kallo, ta koma a hnkli ta kwanta tare da lumshe ido. Ko kadan Khaleel bae ji ddin ynda ya tarar abokanan nasa ke partyn ba duk da yasan yyi abinda ya fi hka, mata ne cakude da maxa ana ta tsiya wasu kuma na ta rawa, ga hayakin cigarette ko ta ina, wutan gun very dim, Najeeb da yyi mugun farin cikin ganin khaleel ya nufe sa da sauri yace "welcm frnd dama kai ake jira " Maska ya nufo sa shima yana yar dariya yace "har na fara shirya irin rashin mutuncin da xan maka wllh" Khaleel yace "ae tun da nace xan xo xan xo, but ban ji ddin gayyatar mata da kuka yi ba nn" hararansa Maska yyi ya bar wajen, Najeeb yace "to in ba a gayyace mata ba meye amfanin partyn. Cum on wani wine xa a kawo maka" Khaleel yace "no, soft drink ma ya isa bana shan wine a waje kai ma ka sani" Najeeb ya hade rae yace "cum on b ur self mana ina kaga alamar soft drink a nn," Najeeb bae jira cewarsa ba ya nufi gun in da drinks suke ya dauko masa wani wine ya kawo masa, Khaleel yace " Kai! So kke in kasa xuwa gida yau ko, ae kasan bana shan irin wa ennan bae kamata ku siyo irin wnn wines din ba ma, sae ku haukatar da mutane cikin daren nn ae, just get me a bit cool one, bana son disgracing kai na yau" Najeeb yyi dariya ya koma ya dauki wine din da yasan Khaleel na sha, ya bude ya tuttulal cikin tumblers din dake ajiye wajen snn ya bude wnda Khaleel yace baya so ya xuba cikin kwalban ya rufe ya kai masa, Khaleel ya karba ya bude ba tare da ya bukaci cup ba ya kafa kai, cire bakinsa yyi da sauri yace "taste din ya canxa, kasan na dde bn sha wnn ba" Najeeb ya daga kafada ya bar g un yana murmushi a xuciyarsa yace "forever xan raba ka da damsel din nn coz she is nt meant for yhu, Khaleel ya ci gaba da shan wine din. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 64..... Khaleel ya dago kai yana kallonsa yace "hka nn kawae me xan je in yi kmr wani mara aikin yi" Najeeb yace "ohh six months bck da kayi birthday dinka baka da aikin yi ne ko?" Khaleel yyi murmushi yace "bani da iyali ne a lkcn, da ina da baxan yi ba" Najeeb yace "cum on, kar kayi mana fuck up guy, kasan Maska won't be happy, ynda kuke da shi kace baxa ka birthday nasa ba is nt fair" Khaleel yyi tsaki ya ci gaba da abinda yake yace "ina ga kai gama aikin da ke gaban ka Yau shi yasa kke interruptn dina" Najeeb ya mike ya fice daga office din yana tunanin ta inda xae ja ra'ayin Khaleel su je birthday din abokin nasu. Karfe takwas da rabi Khaleel ya shigo gida, Ameesha da ke kitchen tana wanke wanke ta fito tayi masa sannu da xuwa xata karbi briefcase din hannunsa yace "don't bother je ki ki ci gaba da abinda kike" sama ya nufa har xae shiga dakinsa sae kuma ya nufi dakin Ashnaah tana kwance tana Duba handout din Chem, kallo daya tayi masa ta mayar da idonta kan abun hannunta, juyawa yyi ya rufe mata kofar ya nufi dakinsa, kasa bacci Ashnaah tayi ranan sae tunanin ynda usman xae yi ya sa Khaleel ya saketa take, ita dae ta ga ynda xa ayi wnn abun. Washegari da safe Khaleel ya xaune dinnin Ashnaah ta sauko da shirin sch, ta nufi dinnin din ta hade fuska tace "na shirya" wani mugun kallo yyi mata yace "kin ma raina ma kanki hnkli yarinyar nn, shi lecture din kullum ake yi da safe" hararansa ta shiga yi tace "da baka sani ba" yace "to bbu inda xa ki yau har sae kin kawo min timetable din ki" da sauri ta bude jakar hannunta ta fiddo timetable din ta ajiye masa gabansa, dauka yyi yana kallo, can ya ajiye ya ci gaba da shan tean gabansa, juyawa tayi ta koma falo ta xauna. Ameesha ta fito daga kitchen din ta nufi dinnin ta ja kujera ta xauna tana kallon Khaleel, daga kai yyi yana kallonta yace "lfya?" Ta dan yi murmushi tace "dama ina son ka bar ni in koma aiki ne plss" ajiye cup din hannunsa yyi ya hade rae yace "amma baki da hnkli, keep dis at d bck of ur mind dat as far as u remain in dis house bbu aikin da xa kiyi, Kinga nayi kama da irin maxa masu barin matansu su yi aiki" hawaye ne ya ciko idonta, ya Mike ya dauki wayoyinsa ya bar dinnin din, Ashnaah da ke xaune falo tayi dariya ta mike tana kallon Ameesha tace "sae kuma kika yi shiru kmr wnda aka dinke ma baki" juyawa tayi ta fice daga falon Khaleel ya bi ta da kallo. Khaleel na haraban hsptl yana xaune da wani patient dinsa suna hira najeeb ya karaso shima ya jawo kujera ya xauna bayan sun gaisa da patient din, patient din ya Mike yyi ma Khaleel sallama ya nufi cikin hsptl, Najeeb yace "Maska ya daga birthdayn sa sbda Kai, I told him u re very busy dis wk ba lallai ne ka samu xuwa ba, nd he decided to let it b on Sunday kaga wk end knn don hka baka isa kace baxa ka ba wllh" yau Sunday Ashnaah ta sauko falo rike da bucket dauke da hijjabanta da ta wanke a bayinta, Khaleel ya juya yana kallonta yace "ina xa ki" tace "shanya xan yi mana" ya mike da sauri yana kuma kallon dan ves din jikinta yace "a hka xa ki fita" ta hade rae tace "to su waye a gidan" wani tsawa ya daka mata ya nufi inda take ta ajiye bucket din da sauri ta bar gun tun kan ya iso tana hararansa, daukar bucket din yyi ya fice daga falon, Ameesha dae na kitchen tana lunch, yana fita da kmr minti biyar aka bude kofar wata mata ta shigo falon da sallama, Ameesha ta fito da sauri daga kitchen ta rungumeta cike da murnan ganinta suka karaso cikin falon, Ashnaah dae sae kallon matar take ko ba a gaya mata ba ta ga alamar uwar Ameesha ce, Matar tace "me kike yi a kitchen" dae dae nn Khaleel ya shigo falon rike da bucket, da mmki yake kallonta yace "Mama ke ce a gidan namu sannu da xuwa" a takaice ta amsa masa ya karaso cikin falon ya gaisheta da ladabi ta amsa bbu yabo bbu fallasa, Ameesha ta juya tana kallon Ashnaah tace "mum dita knn" Ashnaah tace "ae na ga alama ina yini mama" kin amsawa hajiyar tayi, Khaleel ya Mike ya nufi stairs ya ajiye mata bucket dinta snn ya haura Sama. Ashnaah ta tabe baki tace "ikon Allah" juyawa tayi ita ma ta nufi sama, hajiya ta mike tana kallon Ameesha fuskarta a daure tace "mu tafi daki" mikewa tayi suka nufi sama xuwa dakinta, Ameesha tayi shiru tana sauraron irin hudubar da uwar tata ke mata tana digestn, har ta Kai aya snn ta xuge Jakarta ta fiddo wani abu kulle a fallen xani ta hade rae tace "saura kuma don ubanki ki ki yi" Ameesha ta marairaice tace "amma fa ni momy tsoro nake ji" ta ja kunne ta da karfi tana huci tace "don ubanki ki xauna takaicin namiji da matarsa ya kashe ki tunda ke kince yar wahala ce," Ameesha tayi shiru tana kuma nazarin abubuwan da mum dinta ta gaya mata, kuma fa hka ne kila Ashnaahn ma ba xaune take ba don tana mmkin ynda duk irin tsiwan da take na Khaleel baya Mata komae sae dae yyi ta kallonta batun kuma yace mata baya sonta. Karfe biyar na yamma hajiya ta bar gidan, Khaleel na jin fitar ta ya shigo dakin Ameesha yana Mata mugun kallo yace "bna toleratin wnn a gidana in ganin juna kuke son yi to ki dinga shiryawa kina xuwa can gidanku kina samunta," hade rae Ameesha tayi bata ce komae ba har ya juya ya fice daga dakin ta dan yi murmushi a xuciyarta tace xaka gane kuranka. Karfe shidda da yan mintuna Khaleel ya shirya cikin nml dressing dinsa na 3qtre da farar polo ganin ynda abokansa ke ta damunsa da kira, ko kadan bae son ko wannensu ya xo gidansa shi yasa yyi deciding ya tafi kawae, ya fito dakinsa rike da car key dinsa har xae sauka sae kuma ya kuma juyawa ya nufi dakin Ashnaah, bacci ya sameta tana yi, durkushewa gabanta yyi yana kallon fuskarta ya daura hannu a hnkli kan shafaffen cikinta ta bude ido da sauri yyi saurin cire hannunsa ya mike tsaye, mikewa xaune tayi tace "meye hka" juyawa yyi ya fice daga dakin ta bi sa da kallo, ta koma a hnkli ta kwanta tare da lumshe ido. Ko kadan Khaleel bae ji ddin ynda ya tarar abokanan nasa ke partyn ba duk da yasan yyi abinda ya fi hka, mata ne cakude da maxa ana ta tsiya wasu kuma na ta rawa, ga hayakin cigarette ko ta ina, wutan gun very dim, Najeeb da yyi mugun farin cikin ganin khaleel ya nufe sa da sauri yace "welcm frnd dama kai ake jira " Maska ya nufo sa shima yana yar dariya yace "har na fara shirya irin rashin mutuncin da xan maka wllh" Khaleel yace "ae tun da nace xan xo xan xo, but ban ji ddin gayyatar mata da kuka yi ba nn" hararansa Maska yyi ya bar wajen, Najeeb yace "to in ba a gayyace mata ba meye amfanin partyn. Cum on wani wine xa a kawo maka" Khaleel yace "no, soft drink ma ya isa bana shan wine a waje kai ma ka sani" Najeeb ya hade rae yace "cum on b ur self mana ina kaga alamar soft drink a nn," Najeeb bae jira cewarsa ba ya nufi gun in da drinks suke ya dauko masa wani wine ya kawo masa, Khaleel yace " Kai! So kke in kasa xuwa gida yau ko, ae kasan bana shan irin wa ennan bae kamata ku siyo irin wnn wines din ba ma, sae ku haukatar da mutane cikin daren nn ae, just get me a bit cool one, bana son disgracing kai na yau" Najeeb yyi dariya ya koma ya dauki wine din da yasan Khaleel na sha, ya bude ya tuttulal cikin tumblers din dake ajiye wajen snn ya bude wnda Khaleel yace baya so ya xuba cikin kwalban ya rufe ya kai masa, Khaleel ya karba ya bude ba tare da ya bukaci cup ba ya kafa kai, cire bakinsa yyi da sauri yace "taste din ya canxa, kasan na dde bn sha wnn ba" Najeeb ya daga kafada ya bar gun yana murmushi a xuciyarsa yace "forever xan raba ka da damsel din nn coz she is nt meant for yhu, Khaleel ya ci gaba da shan wine din. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 65⃣Daga nesa Najeeb ya xaunayana kallon Khaleel yana murmushi,Faruqh dake xaune gefensa yace"kae baka tsoron Allah koh Najeeb,me gayen nn yyi maka hka kkeneman bugar da shi" Najeeb ya juyaya hade rae yana kallon abokin nasayace "an gaya maka bae saba shabane wnn da kke gani graduate newajen shan giya" mikewa Najeeb yyiya nufi Khaleel ganin ya ajiyekwalban, ya dauka ya ji shi emptydariya yyi yana kallonsa yace"wndrful har ka shanye, a da do makawani" Khaleel da tuni giya ta somaaiki ys gyada masa kai, Najeeb yajuya da sauri sae gashi ya dawo dawata giyar ba irin wnda ya fara kawomasa ba, cikin lkci kankani Khaleel yaballe murfin ya kafa kai ganin shi maneman shanyewa yake yasa Najeebya fixge, Khaleel ya Mike tsaye yanatangal tangal kmr xae fadi cikinmgna irin ta mashaya yace "don mexaka karbe min ruwana" Najeeb yyidariya ya xaunar da shi yace "giyar kadae" dariya Khaleel ya dingakyalkyalewa da kmr wani tababbe,hkn ya ba Najeeb dariya ssae don harya manta rabon da ya ga abokin nasacikin yanayin nn tun suna karatuAbroad, Khaleel xae mike Najeeb yakuma xaunar da shi yace "hira xamuyi dalla ka xauna" Khaleel yaxauna yana dariya yace "to ina hirartake mu yi ta" Najeeb yace "kafadamin meye matsalarka a rayuwaynxu" Khaleel ya kwashe da dariyahar yana neman faduwa cikinmagana hauka hauka yace "ni ynxu faji na nake on top kmr na hau jirgiwllh" Najeeb yace "ae cikin jirgin mamuke" Khaleel xae mike Najeeb yafixgosa yace "to dawo ka gaya minran da xa ka saki matar ka" Khaleel yaxauna da sauri lkci daya ya hade raesae kuma ya fashe da dariya yacewace matar tawa a ciki?" Najeeb yace"fateema" Khaleel ya wani hade raeyace "ae duk duniya bbu wnda nakeso kmr ta, shiga xuciyata ka gani ma"Najeeb yyi shiru snn yace "waccecikinsu wae" Khaleel ya buga tabledin gabansa yana wara manyanidanuwansa yace "Fateema nacemaka mana, ina sonta fiye da rainann, ta min ne, ta hadu yarinyar gaclass ga kyau ga rashin tsoro gacourage, ga ta yar karama sweetsixteeeen, komae nata burrrgeeniyake, waow I so so luvvvv her" yarungume hannayensa hade dalumshe ido yana girgixa kai, najeebda tuni mood dinsa ya canxa ya haderae yana kallonsa, xae mike ya kumafixgosa yace "but kae da bakin ka aekace baka sonta ba class din ka bace,hw cum kuma ka fara sonta" Khaleelya kuma saka dariya har yana nemanfaduwa daga kan kujerar da yakexaune Najeeb ya rikosa, don kansayyi shiru kmr ba shi ke dariyar bayace "ae tun daga ranan da na gacourage da rashin tsoronta da ajintata shige xuciyata taki fitowa" Najeebyace "to wae da wani hukuncin kayiniyyar mata da ka aureta" Khaleel yaxaro ido yace "ohww har ban sontunawa so irritatinggg, forget dat"Najeeb ya dauki drink din da yakwace a hannunsa yace "gashi sharuwan ka ka koshi" fixgewa Khaleelyyi ya shiga kwankwade shi, Najeebya Mike yana murmushi ya bar wajen,ba a dau lkci ba ya dawo rike dapaper da pen yace "rewrite dis letterfor me frnd, ka kuma yi min rubutume kyau idan ba hka ba baxan kai kagun Fateemar ka ba," Khaleel ya ajiyekwalban hannunsa da sauri ya mikeyana tangal tangal yace "ina yakerewrite din yake" Najeeb ya xaunarda shi ya ajiye masa takardungabansa, Khaleel ya fixge pen dinhannunsa yace "wnn ne rewrite din"najeeb yace "recopy t neatly a nnidan ba hka ba bbu inda xan kai ka"da kyar Najeeb ya samu Khaleel yakwafi few words din dake takardanxuwa daya takardan da ba komae,duk da a buge yake hkn bae sarubutunsa ya ki kyan gani ba veryneat, har abun ya ba Najeeb mmki,yyi murmushi yana karanta dancontent din takardan, ko kadan baebari kowa ya lura da abinda kefaruwa tsakaninsa da Khaleel ba duksun samu mata hnkli ya gushe,Najeeb ya Mike ya Duba aljihunKhaleel ya ciro makullin motarsa snnya dagosa yace mu tafi gida toh, dakyar ya sa Khaleel cikin mota donsake masa jiki yyi yana ta abubuwanhauka har yana cewa xae daga motarya kai ta gida kawae, shi dae Najeebbiye masa kawae yake, goma dakusan rabi suka iso gida, ba karaminwahala Khaleel ya ba Najeeb bawajen fito dashi daga mota ba, daganinsa ka ga mashayi bbu kowafalon hakan ya basa daman haura wada shi sama, Ameesha ce ta fito dagadakinta jin shigowar motar Khaleel,tsayawa tayi tana kallonsu, juyawatayi ta koma dakinta cike da takaici,Ashnaah kam har tayi bacci abun ta,har bedroom Najeeb ya kai sa yakwantar da shi snn ya shiga budedrawers dinsa yana dubawa ko xaega alluran da xae masa, ba a dau lkciba yyi masa alluran snn ya kwantarda shi, yana nn tsaye bacci yadaukesa, har da minshari, murmushissae Najeeb yyi snn ya fiddotakardan aljihunsa ya kuma linketaneatly snn ya bude drawernmadubin Khaleel ya ajiye karkashinwani dictionary da ke ciki, ya juya yakuma kallon Khaleel snn ya fice dagadakin. Da asuba wajajen Karfe huduKhaleel ya farka dae dae lkcn daAshnaah ma ta farka ta mike xauneda sauri tunawa da tayi Khaleel baedawo jiya ba har bacci ya dauketa,mikewa tayi ta nufi window tanalekan ko xata ga motarsa, bata gamotar a inda yake parkin ba, hkn yasata nufi kofa xata fita ba tare da tasantakamaiman abinda xata fita yi ba,Khaleel kam yana xaune gefengadonsa ya dafe kansa da yyi masanauyi ssae, lkci daya ya ji cikin sa yahautsine ya mike da sauri yana ganinjiri ya nufi bathroom dinsa kasa shigayyi ya fada nn bakin kofar ya shigakwarara amae, dae dae lkcn daAshnaah ta fito daga dakinta da yakeko ina was very cylnt lkci daya tajikakarin aman nasa, da sauri ba tareda tayi wani tunani ba ta budekofarsa ta shiga ta nufi bedroom dinnasa, durkushewa tayi gabansa arude ta rikoka ta shiga tambayarsame ya faru, warin giya taji ya buge ta,ta kauda kanta da sauri shi kam harlkcn aman bae tsaya masa ba. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 66..... Ashnaah ta koma baya tana kallonsa har ya gama aman taga ya rike kai, dawowa tayi gabansa ta dago kansa a hnkli tana kallon fuskarsa, ya bude Idonsa da ya kada yyi jajir yana kallonta, samun kanta da yi masa sannu murya can ciki tayi, ya shiga kkrin mikewa tsaye yyi baya xae fadi ya rike kofar bayin da sauri, a hnkli ya kuma durkushewa wajen, Ashnaah da duk ta ma rasa abun yi ta matso kusa da shi ta shiga cire masa rigar jikinsa a hnkli tana kallonsa ya rage masa singlet, mikewa taga ya kuma yi ita ma ta mike tana kallonsa da kyar ta iya bude baki tace "ina xa ka" bedroom ta ga ya koma, hkn yasa ta shiga gyara gun da yyi aman, har ta gama snn ta hada masa ruwan dumi dae xae yi wanka ta dawo cikin dakin ta samesa xaune gefen gado ya dafe kai, durkusa wa tayi kusa da shi tana kallonsa tace "na sa maka ruwan wanka" dago kansa yyi yana kallonta bae ce komae ba, can ya mike da taimakonta ya shiga bathroom don yin wanka, kasa fita tayi daga dakin ta gyara masa gadonsa, tana tsaye ya fito daure da towel, dauke kae tayi da sauri, ya karaso gado ya xauna ya kuma rike kae, juyawa tayi tana kallonsa ta rasa takamaiman abinda xata yi, a hnkli ta nufi inda ya ke ta durkusa gabansa murya can kasa tace "baka da lfya ne" ya gyada mata kai kawae yana kallon fuskarta tace "to in kira maka Khadija" girgixa mata kai yyi, hkn yasa ta mike ta nufi wardrobe dinsa ta ciro masa gogaggiyar jallabiyarsa da ta gani, da taimakon ta ya saka, snn yyi kwanciyarsa kan gado nn da nn bacci ya daukesa, Ashnaah dae na xaune gefensa ta kafa masa ido tana kallonsa, Juyawa tayi ta kalli agogo taga an ma kusa kiran sllhn farko, ta dan jigininar da kanta jikin gado nn da nn ita ma bacci ya dauketa nn a xaunen, kiraye kirayen sllh ne ya farkar da ita ta bude idonta ta ganta rungume jikinsa ya kankameta ga jikinsa xafi, daga kai tayi tana kallon fuskarsa suka hada ido don idonsa biyu, ta boye fuskarta a kirjinsa da sauri, taji ya dauro bakinsa a hnkli kan gashin kanta, har lkcn sllh yyi idonsu biyu gaba daya, ita dai kin dago kanta tayi daga kirjinsa, a hnkli taji ya kwantar da ita ya mike ya nufi bathroom ta bi sa da kallo, alwala yyi ya fito ya shimfida darduma nn cikin daki don yin sllhnsa, don bae jin xae iya xuwa masallaci, ita ma ta mike ta shiga bayin tayi alwala ta fito ta nufi dakinta don yin sllh, tana idar da sllh ta kasa xama dakinta hkn yasa ta fita ta koma dakinsa ta ga har lkcn wae sllh yake, ta dae gaji da tsayuwa bae idar ba ta juya ta koma dakinta tana tunanin wani irin sllh ce hka yake, ko da ta dawo dakin ta samu Ameesha durkushe kusa da shi yana kwance gefen gado, juyawa tayi ta fice daga dakin daga shi har Ameesha suka bi ta da kallo. Karfe bakwae da kusan rabi Najeeb ya danna bell, Ameesha da ke kitchen ta fito ta bude kofar, shi ya fara gaisheta ta amsa fuskarta daure, yana murmushi yace "ni kuma meye nawa xa ki daure min fuska kinsan wahalar da mjinki ya bani jiya kuwa, ina gida aka kirani na xo na samesa a buge kinsan jiya birthday din Maska ni dama bn samu xuwa ba" a hnkli Ameesha tace "to Allah ya shiryesa nayi xaton ya ma daina don tun da na shigo gidan nn bn ga ya sha ba" Najeeb yyi dariya yace "xae dae daina, ynxu ya tashi ko ko" Ameesha tace "ehh ya tashi na basa tea kuma nayi masa allura bacci ma yake ynxu" Najeeb yace "to bari in dubo sa, Fateema fa" Ameesha tace "tana dakinta" sama ya nufa don xuwa dakin Khaleel ita kuma ta koma kitchen ta ci gaba da wanke wanken da take. Ashnaah da shigowarta dakin Khaleel knn bayan ta ji saukar Ameesha downstairs ta mike da sauri don duk a tunanin ta Ameeshan ce ta shigo don bata son tana ganinta a dakin, da mmki take kallon Najeeb, ya sakar mata murmushi yace "jinyarsa kike" da sauri tace "no shigowa na knn, shi ma abu na xo dauka" karaso wa yyi kusa da Khaleel yana kallonsa, ya dan taba goshinsa yace "jiya giya ya sha yyi over doze a wani birthday da suka tafi da abokanansa," Ashnaah ta tabe baki bata ce komae ba, Najeeb ya nufi gaban madubin Khaleel yana cewa "idan ya tashi ga magani nan ki dauka ki basa ba don halinsa ba, promise me yhu wil do dat" Ashnaah tace "OK" bude drawern yyi ya saka ledan hannunsa snn yyi saurin fiddo da takardan da ya sa karkashin dictionary ya daura kan dictionaryn ynda dole sae mutum ya gani idan ya bude drawern, ya rufe drawer din ya juya yana kallon Ashnaah ya fada mata dosage din magungunan snn yace "yhu make sure yhu giv him idan ya tashi plss" juyawa yyi ya fita daga dakin ta bi bayansa da sauri har suka fito corridor snn tace "yhu promise me something sometimes ago, nd I have been lookn fwrd...." Murmushi yyi yace "I tried my best sister, my plans didn't go, but kar ki samu damuwa i wil look for another, though kwanaki naji yana fadi cikin frndz ya kusa sallamarki vry soon shi yasa nayi relaxing" Ashnaah tace "to ka dae min kkri pls" murmushi yyi ya gyada mata kai ya juya ya bar wajen, ita kuma ta nufi dakinta, dae dae lkcn da wayarta da ta mance gaban madubi ya katse daga vibration din da yake, da sauri ta nufi gaban madubin ta duba taga mis calls din usman har hudu, kiransa ta shiga yi da sauri, bugu daya ya dauka tare da sauke ajiyar xuciya yace "ina kika shiga hka Ashnaah" ta ce "ina falo ne hope lfya ka kira da sassafe hka" yace "Karfe nawa mijin ki ke fita aiki da safe" shiru tayi kmr me naxari can tace "usman ni fa nace maka lfya nake son mu rabu da shi wat re yhu tryn to do" yace "baki yrda dani ba fateema, I told yhu am doing him no harm" tace "to shknn amma bana tunanin yau xae fita aiki da wuri don bae da lfya, hold on tukunna" ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 67..... Ashnaah ta ajiye wayar hannunta ta nufi kan gadonta jiki ba kwari ta kwanta tare da lumshe ido, duk ta ma rasa me ke damunta, bacci ne ya dauketa nn take. cikin bacci ta ji an bude kofarta lkci daya ta farka ta mike xaune tana kallon kofar, Ameesha ce ta shigo dakin tana kallonta tace "ba kiyi breakfast ba ga shi har tara ya wuce, baxa ki sch bne yau." Ashnaah ta kalli agogo snn tace "xan je, bari inyi wanka" Ameesha tace "OK snn ta juya ta fita" mikewa Ashnaah tayi ta nufi cikin bathroom don yin wanka, cikin riga da skirt dinta ta shirya ta dan gyara fuskarta snn ta daura dankwali ta fita, har ta fara sauka stairs sae kuma ta tsaya tana kallon kofar falonsa , juyawa tayi ta koma sama ta bude kofar ta shiga a hnkli snn ta nufi bedroom dinsa, xaune ta samesa gefen gado yana shan coffee, ya daga kai yana kallonta, ji tayi kmr ta nutse don bata san me xata ce ya kawota dakin ba bata yi tunanin idonsa biyu ba, shi dae bae ce mata komai ba ya ci gaba da shan coffen hannunsa, juyawa tayi da sauri ta nufi gaban madubinsa ya bi ta da kallo, bude drawern tayi idonta ya fara sauka kan farar takardan dake linke neatly kan dictionary ta dauki ledan maganin da xata dauka ta juya tana kallon Khaleel bbu yabo bbu fallasa tace "dama abokin ka ne yace a baka wnn idan ka tashi" kallon ledan kawae yake, hkn yasa ta hade rai ta karasa kusa da shi ta mika masa, karba yyi ya bude yana kallon magungunan snn yace "I've taken drugs ynxu, ki mayar sae anjima" ta karba ta juya ta nufi gaban madubin ta ajiye ledan, idonta ya ku ma sauka kan takardan, rufe drawern tayi ta juya tana kallonsa bbu yabo bbu fallasa tace "xan tafi sch" bai ce komae ba sai shan coffe din hannunsa yake, ta juya xata fita taji yace "ki bari sae gobe" juyawa tayi tana masa wani irin kallo tace "sbda me" ya ce "sbda bbu wnda xae kae ki" bae jira cewarta ba ya mike ya nufi bathroom, tayi tsaki ta juya ta fice daga dakin. Through out ranan Ashnaah a falo suka yini da Ameesha suna ta hiransu duk da Ashnaah hnklinta na gun kallon da take, shi kam Khaleel yana sama, har suka yi azahar Ashnaah bata ga ya sauko xuwa masallaci ba, samun kanta tayi da ce ma Ameesha baki dubo mijinki ba khadija" Ameesha dake cin abinci tace "gwara ke in kin je ba lallai ne ya gwale ki ba, daxu da na shiga Ca yyi ina damunsa bacci zae yi" Ashnaah ta tabe baki tace "ya ce maki hka bare ni karan kada miya". Har aka yi la'asar suna falo ita Ashnaah na kallo Ameesha kuma na danna waya, hudu da rabi Ameesha ta mike tace "bari in daura girki" Ashnaah tace "OK" Ameesha na shiga kitchen Ashnaah ta mike da sauri ta nufi sama, falonsa ta shiga ta karasa bedroom, kwance ta samesa ya lullube da bargo har kansa, ta dde tsaye tana kallonsa daga bisanni ta karasa gadon a hnkli ta durkusa gefensa tana kallonsa, yaye bargon tayi a hnkli suka yi ido hudu da shi ta mike da sauri xata bar wajen ya jawota ta fado jikinsa, ssae jikinsa yyi xafi, ya rungunmeta tare da lumshe ido tayi lamo jikinsa, ganin bae kyaleta ba yasa ta janye jikinta a hnkli daga nasa ta mike xaune amma ta kasa kallon cikin idonsa, murya can kasa tace "ka sha magani" girgixa mata kai yyi ta mike da sauri ta nufi gaban madubinsa ta bude ta dauko ledan maganin ta shiga ballesu kmr ynda Najeeb yace tayi, fridge ta bude ta dauko ruwa snn ta dauki cup din da ta gani kan fridge din ta bude ruwan hannunta ta dauraye cup din da shi ta xubar a bathroom snn ta kuma xubawa ta karaso kusa da shi ta durkusa tana mika masa, da kyar ya karba ya xuba maganin a baki snn ya kora da ruwa, mikewa tayi ta dauki ledan maganin ta nufi gaban madubin da shi xa ta ajiye, farar takardan daxu idonta ya kuma tozali da, hka kawae taji tana son gnin takardan meye, ko don ynda taga an mai linki, ta dauka ta shiga warware shi har ta gama snn idonta ya sauka kan dan guntun content din papern sunanta ta ga boldly a rubuce tun kan ta fara karatun, muryar Khaleel taji yace "wats dat?". Ta juya ta kallesa snn ta mayar da dubanta kan takardan, "Ni ibraheem Khaleel MD na sake ki Fateema saki daya, biyu, har uku, Allah ya game kowa da rabonsa Ma'salam" cak komae na Ashnaah ya tsaya a lkcn tana maimaita abinda ta gani a rubuce jikin takardan" mikewa taga khaleel yyi ya nufo ta ganin bata basa amsar tambayar sa ba don shi dae yasan bae ajiye takarda a nn ba, ta juya da sauri ta fice daga dakin, da gudu ta afka dakinta ta sa ki ta jingina jikin kofar tana mayar da numfashi, kuka ta fashe da tana kallon takardar, na farin ciki ne na bakin ciki ne ta kasa tantancewa, hawayenta ta shiga gogewa a hnkli tana murmushi lkci daya wasu sabbin hawayen na saukowa. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 68..... Da sauri Ashnaah ta bar jikin kofar jin yana bubbugawa ta bude handbag dinta ta saka takardan a ciki snn ta shige bathroom, komawa khaleel yyi bedroom dinsa ya dauko spare key din dakinta snn ya dawo ya bude kofar, bin ko ina na dakin yake da kallo snn ya nufi bathroom ya murda ya ji shi a rufe, daga ciki tace "wae meye ne hka ni ka kyaleni wanka xan yi" bae ce Mata komae ba ya jingina jikin bangon kusa da kofar bayin duk da jirin da yake gani, ya kusa minti sha biyar tsaye a wajen Ashnaah taki fitowa, ita kam bbu abinda take sae hawaye, ta rasa meyasa kuka ya ki tsaya mata, jin shirun yyi yawa yasa ta bude kofar bayin a hnkli ta fito don a tunaninta ya bar dakin, ba karamin kara ta saki ba da ta gansa ta juya da sauri xata koma yyi saurin rikota ya rungunmeta lkci daya, sakar masa kuka tayi ta shiga kkrin kwace kanta yaki saketa yana kallonta yace "me kika dauka a drawerna? ina yake" ta hade rae har lkcn tana kiciniyar kwace kanta tace "da'alla ni ka ka sakeni bn dauki komae ba" kallon cikin idonta ya tsaya yi ta dauke kanta da sauri, ya saketa a hnkli ya juya ya fita daga dakin, Ashnaah ta bi sa da kallo snn ta sulale kasan dakin ta shiga rusa kuka kmr warce aka aiko ma da sakon mutuwa. Har kusan shidda Ashnaah bata mike daga inda take ba sae dae ta daina kukan da take, sae da ta fara jin kiraye kirayen sllhn magrib snn ta mike da kyar ta nufi bathroom ta wanke fuskarta ta fito ta xauna gefen gadonta, duk ta rasa particular tunanin da take a xuciyarta, tana jin an tada sllh ta mike da sauri ta ciro hijab dinta snn ta dauko handbag dinta ta nufi kofa, a hnkli ta tura kofar ta fita ta sauka downstairs, bbu kowa falon hkn ya bata damar fita da sauri, gate a rufe yake bbu ko wani mai gadi a nn, tasan suna masallaci, ta shiga bude gate din da sauri snn ta fice, sauri sauri gudu gudu ta nufi bakin titi ta sayar da adai daita sahu ta gaya masa inda xata snn ta shiga. Bakwae da kusan rabi Ashnaah ta isa kofar gidansu, ta fiddo kudinsa ta mika masa snn ta nufi gate dinsu, a sanyaye ta karasa cikin gidan tana kallon motar Abbanta da ke Parke, a hnkli ta tura kofar falonsu ta shiga bata samu kowa falon ba ta nufi sama da sauri ta bude dakin mum dinta ta shiga, xaune ta sameta kan darduma caxbi a hannunta, da mmi take kallon Ashnaah, Ashnaah ta sakar mata murmushi tace "sannu momy bari in yi alwala" bathroom ta nufa da sauri tayi alwala ta fito snn ta tada sllh, sae da ta idar snn momy ta juya tana kallonta da mmki tace "daga ina hka" Ashnaah ta kirkiro murmushi tace "ya xo gun wani frnd dinsa ne a nn wajajen shine nace ya bar ni in karaso gida" momy bata ce komae ba, Ashnaah ta gaisheta amsa tana kallon yar tata, ko kadan Ashnaah bata Bari momynta ta lura da komae ba, tace "Abba na nn ko momy" momy tace "yana dakinsa" Ashnaah bata tambayi yar uwarta ba don tasan tana gidan inna, tambayarta momy tayi ko ta ci abinci Ashnaah tace ta ci, don bata jin cin komai, har tara da rabi, momy bata ga Ashnaah na cewa xata tafi ba, momy ta shigo dakinta tana kallonta tace "wae ba yau xaki koma bne, kinsan Abbanku fa bae san kin xo ba" Ashnaah tayi shiru snn tace "sae gobe momy" momy tace "to tun da kwana xa kiyi ki tafi ki gaida Abban ku kar ya gan ki gobe ya xame min abun mgna" Ashnaah ta gyada ma mum dinta kai kawae, momy ta juya ta fita, kuka Ashnaah ta shiga rerawa a hnkli tana tunanin ynda iyayenta xasu dauki xancen da ta kawo masu. Khaleel kam na dawowa daga masallaci ya nufi dakin Ashnaah, bae sameta a ciki ba hkn yasa ya nufi bathroom nn ma bata nn, fitowa yyi ya shiga dakin Ameesha ya sameta xaune kan darduma, yace "fateema fa" Ameesha tace "tun hudu ta hau sama, tana dakinta" juyawa yyi ya fice daga dakin, bbu inda bae duba ba a gidan amma bae ga alamar Ashnaah ba hnklinsa yyi mugun tashi, to ina ta tafi da daren, masu gadi ma suka ce basu ganta ba, sama ya koma ya dauki makullin motarsa ya sauko, rasa inda xa shi nemanta yyi, lkci daya ya shiga tunanin to takardar meye ta gani daxu ta ki ba sa, gidansu ya nufa kawae goma saura qtr ya isa kofar gidansu, ya fito ya nufi gun mai gadi, bayan sun gaisa ya ke tambayarsa ko Ashnaah ta xo, yace masa eh, sae da ya fara sauke ajiyar xuciya snn yace "to ka min mgna da ita don Allah" mai gadi ya nufi cikin gidan, Abba ne ya bude kofar yana kallon mai gadin yace "ya aka yi Musa" mai gadin yace "wae mai gidan fateema ne ke jiranta a waje" Abba yace "wace fateemar" Mai gadin yace "fateema dae" juyawa Abba yyi ya nufi sama ya bude kofar momy fuskarsa a daure yace "me yarinyar nn ta xo yi gidan nn yau ba tare da na sani ba" Momy ta hade rae tace "bn gne me ta xo yi ba" fada ssae Abba ya shiga yi yace "ta xo ta fice masa daga gida mijinta na jiranta a waje" Ashnaah da ke jin duk abinda abbanta ke cewa ta shiga kuka a hnkli tasan dole ta fada masu me ya dawo da ita gida, mikewa tayi tun kan ya shigo inda take ta dauki hijab dinta da takardan sakin da ta gani ta fita a sanyaye don xuwa jin me ke tafe da Khaleel kuma. Yana tsaye jikin motarsa ta fito daga gate dinsu, kallonta kawae yake har ta karaso inda yake snn ta rungume hannayenta fuskarta daure tace "ina jin ka" kallonta kawae yake har lkcn ya ma rasa me xae ce mata, ganin hkn yasa tace "in baka da abin cewa xan koma cikin gida pls" a hnkli taji yace "me nayi maki Fateema" ta daga kai tana kallonsa don bata ma san ya san sunanta ba, sunkuyar da kanta tayi da sauri don kar ya ga hawayen dake kkrin taruwa idonta tace "me kuwa ka min baka min komae ba" shiru taji yyi bae ce komae ba hkn yasa ta fashe da kuka ssae ta mika masa takardan hannunta, karba yyi yana kallon takardan, cikin sakwannin da ba su wuce sha biyar ba ya gama karanta content din, lkci daya komae nasa ya tsaya ya sake takardan hannunsa ya fadi kasa yana furta innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Ashnaah ta duka ta dauki takardan tana share hawayen fuskarta lkci daya tana murmushi tace "nd am very happy coz I have been lookn fwrd to a day like dis, am vry glad I saw it, dama baka so na bana..." Kasa karashe mgnr tayi sbda kukan da ya ci karfinta, da kyar Khaleel ya iya bude bakinsa da yyi masa nauyi murya can kasa a sanyaye yace "wllh summa tllh bni na rubuta takardan nn ba fateema" da sauri Ashnaah ta juya ta nufi gate dinsu, kiranta ya shiga yi don kasa binta yyi har ta shige gate dinsu, hade kansa yyi da mota yace "No! no, waye yyi min hka" lkci daya hawaye ya cika idonsa. Ashnaah na shiga falon su ta nufi falon Abbanta jiki ba kwari rike da takardan a hannunta, xaune ta same sa da momy, ta durkushe nn tsakiyar falon tana kkrin mayar da hawayen da ke neman xubo mata tana kallon iyayen nata, kasa daurewa tayi ta fashe masu da kuka ssae. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 69..... Kallonta kawae iyayen nata suka tsaya yi, momy tayi karfin halin tambayarta lfya, shi dae Abba bae ce komae ba sae kallonta kawae yake, kasa cewa komae Ashnaah tayi sae kukan da take kanta a kasa, mikewa momy tayi ta nufi inda take tana kallon takardan hannunta ta karba, momy na gama karanta content din ta juya a sanyaye tana kallon mai gidanta, Abba yyi murmushi yace "har ya sako ta knn koh, dat's gud" Momy ta dauke kanta tana kkrin mayar da hawayen idonta ta dago Ashnaah suka nufi sama, kasa ba momy amsan tambayoyin da take ta ta jero mata Ashnaah tayi, hkn yasa momy bata kuma ce mata komae ba ta mike a sanyaye ta fice daga dakin, ko da ta koma falo bata tarda mai gidan nata ba, hkn yasa ta nufi bedroom dinsa, ta same sa xaune yana Danna laptop, ya dago kai yana kallonta yace "ynxu abinda nake so da ku shine, ku tabbatar ita daya take, don in har tana da juna biyu to wllh wllh baxata xaunar min a gida ba ina ganinta ina ganin takaici." Cikin fushi momy tace "halan tana da wani gidan uban ne bayan wnn, in tana da ka fada min in kai ta" cikin kuka ta karashe masa mgnr Abba yace "ni dae na gaya maku wllh." Ikon Allah kadae ya kai Khaleel gidansu wajen karfe goma da rabi, mai gadi yyi mmkin gninsa da daddare hka da yake suna shiri ssae, khaleel ya nufi cikin gida a birkice ba tare da ya ma san mai gadin na gaishesa ba, bbu kowa falon ya nufi dakin mum dinsa da sauri, ya sameta tana shirin kwanciya, da mmki take kallonsa tana kallon agogo, ganin yanayinsa ya kuma rudar da ita don tafi kowa sanin dan nata, ya xauna gefen gadonta tare da dafe kansa, ta karaso da sauri tana kallonsa tace "me ya faruwa Khaleel" ya dago kai yana kallonta, kasa ce mata komae yyi sae ga hawaye, ummi duk ta rude ta xauna gefensa tace "tok 2 to me son, me ya faru" da kyar khaleel ya iya bude baki ya gaya ma umminsa abinda ya faru, ya karashe mgnr cikin tashin hnkli kmr xae fashe mata da kuka yace "ku taimakeni plss mum, wllh bni ne na rubuta takardan ba ban san da shi ba " still Ummi tayi tana kallonsa da mugun mmki, Khaleel ya sauko kasa ya durkusa nn gabanta a raunane yana rike da kafafuwanta yace "plss Ummi na help me, idan Fateema ta nuna ma iyayenta wnn takardan I knw its over plss ummi" Ummi da duk kanta ya gama daurewa tace "ikon Allah," kwantar masa da hnkli ta shiga yi tace "shknn ka kwantar da hnklinka son Allah na tare da Mae gaskiya, ynxu ka tashi mu tafi gun abbanka muyi masa bayani, gobe sae su tafi can gidan har da kai." Washegari da safe har gida Abba ya kira likita ya gwada Ashnaah ko tana da juna biyu, likitan yyi gwaje gwajensa yace bbu komae, ita dae Ashnaah bbu abinda take sae hawaye duk ta rasa me ke mata ddi a duniyar, bayan likitan ya tafi Abba yasa momy ta kira mashi ita, ta sauko kasa a sanyaye ta durkusa falon Abbanta tana kallonsa tace "Abba gani" Abba ya maida hnklinsa kanta yana kallonta da kyau yace "a ina kika san mutumin nn, kar kuma ki kuskura ki min karya" hawaye ne ya shiga bin kuncinta, ta juya tana kallon momynta da ke kallonta, a sanyaye ta shiga gaya masu abinda ya hadata da Khaleel har ya aureta, bbu abinda ta boye masu har irin xaman da suka yi har ixuwa jiya da ta ga takarda a drawernsa, Abba yyi murmushi yace "wndful! dats gud, yhu c ol dis happen to u as a result of dis obeyin me, but na ji ddin da hkn ya faru, I knw you've learnt a great lesson frm now on, don hka in xa ki mayar da hnkli a karatu ynxu ki maida" kuka ssae Ashnaah take gashi ita dae har lkcn ta rasa gane dalilin kukanta, Abba ya dauki wayarsa ya kira wani abokinsa mai babban motar daukan kaya yace ya ara masa xa a kwaso masa wani kaya ne, da sauri Ashnaah ta daga kai tana kallonsa kukan da take ya karu ssae, Abba yace "ni bance kiyi min kuka ba, ki tashi ki tafi Allah xae saka maki duk da ke ce baki jin mgna, ynxu sae ki mayar da hnklin ki a karatu in kin ga dama, ga yar uwarki nn har tayi nisa" da kyar Ashnaah ta mike jiri na kwasarta ta nufi sama ta fada kan gado ta dinga rusa kuka kmr ranta xae fita. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 70..... Karfe sha daya da yan mintina Alhaji Muhd mahaifin Khaleel da wasu daga abokansa da shi kansa Khaleel din suka iso gidansu Ashnaah, hka kawae gaban Khaleel ke faduwa, Abbansa ya fito da sauran abokansa biyu da kaninsa yana kallon Khaleel yace "to ae sae ka fito ka makale cikin mota" Khaleel ya girgixa kansa da kyar yace "bana son shiga Abba" Abokin abbansa yace "ka ji sha shanci to sae mu ce masu me in mun shiga, ka fito mu shiga ayi abinda ya dace my frnd" da kyar Khaleel ya iya fitowa daga motarsa, iyayen nasa suka nufi gun mai gadin dake xaune bakin gate din yana biye da su a baya, kanin Abbansa ne ya tambayesa ko mai gidan na ciki bayan sun gaisa mai gadin ya amsa masa da ehh, snn yace to ayi masu sallama da shi, ba a dau lkci ba mai gadin ya dawo ya ba su ixinin shiga yyi masu iso har falon Abba, Abba dake xaune falon ya mike ganin bakin nasa ya tarbesu ynda ya kamata, tsaf ya gane su barin da ya ga Khaleel, Khaleel kam kasa kallonsa yyi kansa a kasa ya gaishesa, Abba ya amsa bbu yabo bbu fallasa, snn khaleel ya xauna kasa nn gefen Abbansa, bayan an gama gaggaisawa abokin dad din Khaleel Alhaji umar yana kallon Abban Ashnaah yace "to dae ba wani abu ne ya kawo mu nn ba illa mun xo ne mu baka hkuri on behalf of dan mu akan abinda ka gani Alhaji, duk da dae shi wnn yaro yace ba shi yyi sakin ba, xancen dae ga shi nn kmr na wasan yara don ba mu taba jin inda mutum xae ce ba shi ne ya saki matarsa ba bayan ga takarda nn a dakinsa, to ynxu dae muna rokon ka afuwa da ka dubi girman Allah kayi hkuri xa mu mayar da yar ka....." Abba da tun da ya fara xancen yake kallonsa da mmki yyi saurin katse sa yana kai wa nn ta hanyar cewa "dama ashe idan aka yi saki uku mace na komawa dakinta ban sani ba" shiru suka yi duk suna kallonsa, Alhaji umar ya kalli Khaleel da sauri yace "saki uku ne dama" Shiru Khaleel yyi bae ce komae ba, da ka gansa kasan he is nt his self, Abbansa yyi tsaki yace "amma kai fa mutumin bnxa ne, dama kasan saki uku ne xa ka sa mu kwaso jiki mu xo nn kmr wasu kananun yara" da kyar Khaleel ya iya bude baki kmr xae masu kuka yace "wllh Abba bani ne nayi sakin nn ba" daya abokin Abban Khaleel yace "to ae Alhaji in har a lkci daya yyi saki ukun saki daya knn a musulince, ko ba hka ba" Abban Ashnaah yyi murmushi yace "idan ka ce ma mace ka saketa saki daya, biyu, uku, to ta saku knn gaba daya ko ba hka yake ba," kai kawae suke gyada masa, Abban Ashnaah yace "to a hka dan ku ya rubuta sakin" Khaleel ya dafe kansa yana ganin wani jiri daga xaunen da yake lkci daya hawaye ya cika idonsa, Abba ya sauke ajiyar xuciya yana duban Abban Ashnaah yace "ina takardan yake Alhaji, ko xa mu iya ganinsa" Abba ya mike ya nufi sama, Alhaji umar ya juya yana kallon Khaleel yace "kaga fa kar ka mayar da mu kananan mutane a nn Khaleel, ko kana shaye shaye ne wae" a raunane Khaleel yace "wllh wllh Abba bani ne na rubuta takardan ba, ban saketa ba ku yrda dani, its a set up I think" shiru duk suka yi suna kallonsa kowa na nasa tunanin a xuciya, Abba ya sauko rike da takardan ya mika masu ya koma ya xauna, warware takardan dad din Khaleel yyi lkci daya ya juya yana kallon Khaleel da mmki fuskarsa daure yace "whose writtin is dis" Khaleel ya xaro ido yana kallonsa gabansa na wani mugun faduwa, Abba ya jefa masa takardan ya dauka da sauri don ko kadan shi bae lura ma da rubutun ba ranan da Ashnaah ta basa, sake takardan yyi ya fadi kasa da wani irin shock, Abbansa da tuni ransa yyi mugun baci yace "lallai ka cika mahaukaci khaleel, kar ka raina mana wayo a nn, ka ga mun yi kama da yara ko marasu sanin ciwon kai, be careful fa" mikewa yyi a fusace yana kallon abokansa yace "plss ku tashi mu tafi, Allah ya ba mu alkhairi Alhaji" rikice masu Khaleel yyi ya dinga rantse rantse shi ba shi ya rubuta takarda ba, ya xamar masu kmr wani xautattce, Abban Ashnaah yyi murmushi yace "to ko da saki daya dan ku yyu ma 'ya ta banga dalilin da xan bari ta koma gidansa ba sae dae muje duk inda xa mu, ku dan ban lkcinku ku saurari abinda yasa nayi wnn furucin ba cin fuska ba" komawa Abban Khaleel yyi ya xauna, Abba ya shiga masu bayani a nutse ynda aka yi Khaleel ya auri Ashnaah snn ya kara masu da duk bayanin da Ashnaah tayi masa daxu, Abban Khaleel ya mike yana murmushi yace "ae hkn dai dai ne, kuma Alhmdllh da ta ga takardan, Allah kuma yyi mata sakayya" sallama yyi masa snn suka fice da abokansa da duk suma xancen bae masu ddi ba suka bar Khaleel nn xaune, da kyar ya isa gida a motarsa yana ganin double double, umminsa dake falo ta mike a rude yanayin da ta gan dan nata, ya xube nn gabanta ta duka da sauri tace "ya aka yi kuma? baku je bne?" daura kansa yyi a kafadarta ya shiga hawaye, rungumesa tayi a rude tace "ka gaya min ya ku ka yi son" kasa cewa komae yyi, hkn yasa ta dago sa suka nufi sama ta shiga bedroom dinta da shi ta sa ya kwanta ta xauna gefensa, ba a dau lkci ba bacci ya daukesa tayi shiru tana kallonsa, tasan jiya kwata kwata bae runtsa ba don a dakinta ya kwana, komawa falo tayi a sanyaye ta ci gaba da abinda take, can wajen azahar Khaleel ya tashi, sae da ummi ta tilasta masa ya ci abinci ya sha tea snn yyi sllh. Tana xaune gefensa bayan ya idar tace "ka gaya min ynda aka yi son" a sanyaye murya can kasa yace "mum its a set up, I knw it is, da writtin dina aka yi rubutun no body will blive I wasn't d one dat wrote it...." Kasa ci gaba yyi ta dalilin tokarewa da muryarsa yyi, lkci daya idonsa ya kada ssae, yana girgixa kai yace "I dont think xan iya rayuwa ba ita Ummi na ku taimake ni plss" hawaye ya gangaro idonsa, hawaye ne ya cika idon Ummi a hnkli tace "wa kke tunanin xae maka hka," shiru Khaleel yyi kmr me naxari snn ya mike tsaye da sauri yace "Ameesha! Ita kadae ta iya kalan rubutu na," makullin mota ya dauka da sauri ya fice daga dakin Ummi ta bi sa da sauri har kasa tana kiransa amma tuni ya shige mota ya figi motar yana danna horn aka bude masa gate ya fice a guje. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 71..... A waje Khaleel yyi parkin bae ko kalli masu gadin da ke gaishesa ba ya nufi cikin gidan da sauri, bae samu kowa a falo ba ya nufi sama fuskar nan tasa bbu alamar rahama ya bude kofar Ameesha, xaune ya sameta gaban madubinta idon nn nata yyi jajir da ganinta kasan ta ci kuka, ya nufeta ya fixgota lkci daya ya watsa mata wasu tagwayen mari masu lfya yana huci yace "ke kika rubuta takardan saki ki ka ajiye dakina don fateema ta gani ko, ki fada min me nayi maki a rayuwa kika min hka, duk halaccin da na maki na aure ki duk da ba son ki nake ba da wnn kaxamin aikin xa ki biya ni is dis my reward? I knw uwar ki ce ta sa ki 3dayz bck da ta xo, confess dat kar in hallakaki" cikin tsawa ys karashe mgnr lkci daya ya kuma watsa mata wani marin ya hade ta da bango yana huci idonsa yyi ja ssae, cikin kuka ssae muryarta baya fitowa ssae take cewa ban gane me kke nufi ba Khaleel, hw dare yhu xaka dinga duka na me nayi maka, bata rufe baki ba ya shaketa, ba karamin wahala ta sha ba ranan don dukan fitan hnkli ya mata, duk ya xama kmr wani mahaukaci, ya fice daga gidan. Ashnaah na xaune dakinsu ta jingina da gado Ashfah ma na xaune sae hiran film din da ake a tv take mata, ko kadan Ashnaah bata san me yar uwartata ke cewa ba, tayi xurfi cikin tunanin da take Ashfah ta dafa kafadarta jin ta kirata ya fi sau uku bata san tana yi, a dan tsorace Ashnaah ta dawo daga tunanin da take ta ce "me kika ce" Ashfah tace "Haba sister, wae tunanin meye hka kike, ain't yhu happy kin dawo cikinmu ynxu, wats ur prblm plss tel me" Ashnaah ta kirkiro murmushi tace "nothin sister just thinkn of my past" Ashfah tace "forget dat plss its nt worth rememberin, ko baki yi farin cikin dawowa cikin mu bne" Ashnaah tayi murmushi tace "am happy sister" Ashfah tace "to bana son in kara ganin kin yi shiru hka pls" Ashnaah ta gyada mata kai kawae, dai dai nn wayar Ashnaah ya shiga vibrate, Ashfah ta miko Mata ta karba a sanyaye tana kallon screen din, usman ta gani ta mika ma Ashfah tace "ki ce ina wanka bana cikin mode din mgna" Ashfah ta karba tayi ynda tace mata snn suka yi sallama suka ajiye wayar, Ashnaah ta dubi Ashfah tace "har an kawo kayan nawa ne?" Ashfah tace "wae masu gadin basu Bari ba wae mai gidan baya nn" Ashnaah bata ce komae ba, Ashfah tace "wae Abba yace mu je ki gaida inna anjima" kai kawae Ashnaah ta gyada mata, aka bude kofar dakin momy ta shigo tana kallonsu tace "abincin waye har ynxu a kitchen," Ashfah tace "na Ashnaah ne wae bata jin yunwa" momy ta hade rae tana kallonta tace "wae wani abu na damun ki ne, ina fa sane da safe baki yi wani kwakwakkwaran kari ba," mikewa Ashnaah tayi tana kirkiran murmushi tace "kallo mu ke ne momy ynxu xan je in dauka" ta gefen momynta ta bi ta fita, momy ta bita da kallo snn ta juya tana kallon Ashfah tace "wae me tace maki ke damunta" Ashfah tace "ynxun nn na gama tambayarta tace wae kawae past take tunawa" momy bata ce komae ba ta juya ta fita. Ashnaah ta sauko downstairs ta nufi kitchen don daukar abincinta da ya kusa awa hudu a ajiye don har an kusa gama na dare, bin ta da kallo Abbanta yyi, ta fito daga kitchen din rike da abincinta xa ta koma sama ys kirata, a sanyaye ta karaso falon ta duka ta amsa tana kallonsa, ya ajiye remote din hannunsa yana kallonta yace "kina da damuwa ne Fateema" ta girgixa masa kai tace "A'a Abba daga bacci na tashi" Abba yace "ok, gobe sae ki shirya driver ya Kai ki sch, kun kusa fara jarabawa ko?" Ta gyada masa kai tace "eh sae next wk xa mu fara wae, amma ynxu sae upper wk" yace "to shknn ki dage da karatu kin ga an wuce ki ssae u have to work hard to meet up" ta gyada masa kai tace "in sha Allah Abba" mikewa tayi ta dauki plate din abincinta ta nufi sama. Khaleel na komawa gida ya shige bedroom dinsa ya saka key ya shiga neman layin Najeeb, bugu daya ya daga, a raunane Khaleel ya shiga cewa "I need yhu plss ka xo ynxu Najeeb" bae jira cewarsa ba ya kashe wayar ya dafe kansa dake juya masa. "Ae ni bbu abinda xan ci gaba da ce maki da ya wuce Allah ubangiji ya kara maki, banxa kawae da bata yo halina ba, me gare Khaleel da har kika nace masa? Ya nemi kashe mana ke, ae sae naga uban da ya tsaya ma Khaleel a garin nn, xae san ya taba min ya ta, sae inda karfin ya kare wllh" cewar mahaifiyar Ameesha ga Ameesha dake kwance bbu abinda take furtawa sae wayyo Allahna, Alhaji mukhtar da ke xaune Sae girgixa kafa yake shi ma fuskar nn tasa a daure ya mike ya dauki wayarsa ya fice daga dakin. Najeeb yyi shiru yana kallon Khaleel bayan ya gama jin bayaninsa, Khaleel ya dafe kansa har lkcn yana hawaye a sanyaye yace "plss don't b surprise frnd, wllh ni kaina nasan na kamu da son fateema da dde wa, help me plss give me a solution to dis prblm I beg yhu" dafa sa Najeeb yyi a hnkli yace "its OK frnd, ka bani address din su Fateeman, I will c wat to do" nan Khaleel ya basa Address dinsu Ashnaah, Najeeb ya kwafe a wayarsa snn yace "amma me yasa xaka xarga Ameesha har ka doketa, idan ba ita bace ba fa" Khaleel yace "don't tell me dat, ita kadae ta iya rubutu kmr nawa, snn bayan ita bbu mai shigar min daki, to wae ma mu nawa ne a gidan da xaka ce kar in xargeta, ko kwana biyar fa ba ayi da xuwan uwarta gidan ba abun nn ya faru, to wa ya sa ta idan ba ita ba" Najeeb ya mike yana kallon abokin nasa yace "kar ka damu frnd ka kwantar da hnklinka, gobe xan tafi can gidansu fateeman." ~Dr khaleel~ By khaleesat Haiydar 72..... Nan Najeeb yyi masa sallama ya fita, Khaleel ya fada kan gadonsa ya runtse ido, duk ji yyi duniyar tae masa xafi, Ashnaah da komae nata kadae ke masa yawo a ka, nn da nn ya ji kmr xaxxabi xae rufesa. Karfe shidda saura na yamma Abban Khaleel ya shigo gida ya nufi dakin Ummi fuskarsa a daure yana kallonta yace "ina ibraheem" da kmr baxa ta ce komae ba sae dae tace "me ya faru kuma" cikin tsawa yace "nace yana ina" bae rufe baki ba Khaleel ya shigo dakin kmr wani mara lfya a sanyaye yace "gani Abba" kallonsa Ummi ta tsaya yi ganin ynda ya wani rame lkci daya, Abba ya juya yana kallonsa a fusace yace "don uwar ka wae halan kana shan giya ne" shiru Khaleel yyi bae ce masa komai ba, Abba ya daka masa tsawa yace "ka fada min me yarinyar mutane tayi maka ka ne mi kasheta yau" fada ssae Abba ke yi kmr xae maresa shi dae Khaleel bae ce komae ba hka ma Ummi, Abba ya gaji don kansa ya juya ya fice a fusace, Khaleel ya daga kai ya kalli mum dinsa snn ya juya ya fice daga dakin. Yana shiga dakinsa da minti goma kiran dad din Ameesha ya shigo wayarsa, da kmr baxae daga ba sae kuma ya daga yyi masa sallama, ba tare da ya amsa ba yace "ka xo gida ka same ni" bae jira cewar Khaleel ba ya katse wayar, sae da aka yi sllhr magrib Khaleel ya samu umminsa yace xae fita snn ya kama hanyar gidansu Ameesha, xaune ya tadda iyayen nata a falo da yayyinta maxa, Abbanta kadae ne ya amsa gaisuwarsa, ya xauna kasa yana kallon Abban nata bae dae ce komae ba, Alhaji mukhtar yace "wato da abin da xa ka biya mu knn ko Khaleel, dats great" takarda da pen ya dauka ya jefa gaban Khaleel yace "bani takardan ta ynxu" daukar takardan Khaleel yyi da pen cikin minti daya ya gama rubutun da yake ya dauka ya risina ya mika masa, karba yyi yana duba content din takardan kmr hka, "Ni Muhd Khaleel na saki khadija saki daya" Alhaji mukhtar yyi murmushi ya dauki wani takardan yyi rubutu yyi sign snn ya mika ma Khaleel, khaleel ya karba ya shiga duba rubutun, sack letter ya gani, mikewa yyi ya cukuikuye takardan ya jefar nn tsakiyar falon yace "sae da safen ku" snn ya juya ya fice daga gidan, mum din Ameesha tace "duk inda xaka neman aiki baxa ka samu matsayin da ka rasa ynxu ba sha sha sha kawae mahaukaci me gare ka xaka walakanta yar mi" Khaleel na shiga motarsa ya hade kae da steering xuciyarsa na masa wani irin xugi, yes tunda ya rasa Ashnaah komae ma ya rasa, wasu hawaye ne suka shiga sakko masa, duk duniyar yaji tayi masa xafi ya rasa me xae yi ya ji ddi, y him?" Da kyar ya iya jan motar ya bar layin, har ya kama hnyar gida yyi tunanin xuwa layinsu Ashnaah ko Allah xae sa su hadu, yana shiga layinsu cikin ikon Allah ya gansu ita da Ashfah sun dawo daga gidan inna knn. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 73..... Parking Khaleel yyi daga gefe ya fito da sauri ya nufo su, kamshin turarensa kawae Ashnaah ta shaka ta juya da sauri tana ganinsa ta ruga a guje ta nufi gate dinsu da sauri, Da mugun mmki Ashfah ke bin Ashnaah da kallo har ta shige gate din kawae gani tayi ta kwasa a guje ba dalili, juyawa tayi da sauri don ganin me take ma gudu, suka yi ido hudu da Khaleel ita ma ba sae ta ruga a guje ba, bin ta yyi da sauri ya shiga kiranta yace "don Allah don Annabi ki tsaya sister," kasa ci gaba da gudun ta yi ta ja burki ta tsaya ba tare da ta juyo ba, karasowa yyi inda take da sauri ya marairaice mata yace "Plss kanwata, kice da fateema tayi hkuri ta saurareni ko na minti daya ne plss help me beg her" Ashfah ta rasa abun cewa can dae tace "to bari in je in mata mgna" da sauri yace "yauwa kanwata ngd ssae ina jira plss" ta gyada masa kai ta nufi cikin gidansu, dakinsu ta samu Ashnaah kwance tana ta rusa kuka, ta karaso da mmki tana kallonta tace "meye abun kuka kuma sister, Kinga fa ni bana son hka, don me xa ki dinga daga min hnkli ne" Kmr ta kara tunxurata ta kuma fashewa da wani matsanancin kukan, Ashfah ta nemi gu ta xauna fuskarta dauke da damuwa tace "don Allah Ashnaah ki daina kukan nn wllh bana so yana damuna" da kyar ta lallasheta tayi shiru sae a snn ta tambayeta a sanyaye ko Khaleel ya tafi, Ashfah ta dan yi shiru snn tace "ehh ya tafi" komawa Ashnaah tayi ta kwanta tare da lumshe idonta kmr mai shirin bacci, Ashfah ta lulluba mata bargo tace "kiyi baccin ki kawae" Washegari da safe driver ya wuce da Ashnaah makaranta kmr ynda Abba yace, ko kadan Ashnaah bata gaya ma kawayenta abinda ke damunta ba kmr ynda suka bukaci sani, through out lectures din ranan shiru kke jin Ashnaah, lectures din ma ba fahimtarsu take ba kwata kwata, Karfe uku da rabi suka ga lectures Ashnaah ta dauki Jakarta ba tare da ta jira kawayen nata ba ta fito don jiran drivernta don tasan at anytime xae xo tunda ta fada masa lkcn tashin su, motar usman ta hango ta dauke kai da sauri amma har ya ganta, ya karaso inda take snn ya fito daga motar da damuwa yace "y ain't yhu pickn my cal Ashnaah" Ashnaah tace "to ina lecture din xan yi pick din cal dinka," shiru yyi yana kallonta, hkn yasa ta dan saki ranta tace "lecture muke ne wllh ka ga fitowa ta knn" yace "bbu damuwa, ya kike ya gida" tace "Alhmdllh" yace "ynxu xa a xo daukarki ko" ba tare da ta kallesa ba tace "ehh" ya dan yi shiru snn yace "kin ko gaya min lkcn da mijin ki ke fita da safe Ashnaah, koh kina ga...." Da sauri ta katse sa tace "ka ga ni fa we re no longer togeda, ya bani takardata tun shekaran jiya ina gidanmu" da mugun mmki Usman ke kallonta yace "waow re yhu serious dear shine baki gaya min ba, waww am so..." Da sauri Ashnaah tace "ka ga, sae mun yi waya ga driver can ya xo" bata jira cewarsa ba ta nufi gun motar gidansu da sauri don ba karamin farin cikin xuwan drivernsu tayi don ko kadan bata son jin mai usman ke shirin cewa. Karfe hudu da kusan rabi Ashfah ta sauka daga a dai daita sahun da ya ajiyeta dai dai bakin gate dinsu, da ganinta kasan daga makaranta take, Najeeb da ke jingine jikin motarsa can nesa da gidansu ya karaso da sauri ganinta, sallama yyi mata ta juya tana kallonsa, wani irin kallo tayi masa xata shiga gida ya sha gabanta da sauri yace "ki saurara pls fateema" Ashfah tayi tsaki tace "ni ba fateema bace malam ka bani hanya" xae yi mgna sae ga Ashnaah ta fito daga cikin motar da yyi parkin gefensu don drivern yace baxae shiga ciki ba momy ta aikesa kasuwa, juyawa Najeeb yyi yana kallon Ashnaah snn ya kuma juyawa ya kalli Ashfah da mugun mmki, kallo daya Ashnaah tayi masa ta dauke kai ta karasa xata shiga gida, Ashfah kam tuni har ta shige gida. Najeeb yace "wait plss fateema" juyawa tayi tana kallonsa, sae kuma ta tsaya don jin me xae ce, ya karaso inda take da sauri yace "dama ku yan biyu ne" juyawa Ashnaah tayi xata shige gida ganin tambayar bae da ma'ana, yyi saurin cewa "ki saurareni plss fateema" Ashnaah ta kuma juyawa tana kallonsa tace "ka ga idan ba ka da abun cewa ka rabu dani don bana son Abbana ya gani tsaye a nn" Najeeb yace "OK but mgnr na da tsayi, ko in bari da nyt" ta daga kafa tace "Allah ya kai mu" snn ta shige gida. Ana sllhn magrib Ashnaah ta sauko kasa ta samu mai gadinsu tace "don Allah baba xan yi bako kuma bana son abbana ya sa ni, anjima kadan xae xo idan ya xo ba sae ka shigo ba kawae ga nmbrta ka min flashn sae in san ynda xan fito" Mai gadin yace "to shkkn" snn ta ba shi nmbrta ta koma cikin gida. Khaleel na kwance dakinsa idonsa lumshe kmr mai bacci aka bude kofa Najeeb ya shigo, bude ido Khaleel yyi a hnkli duk a tunaninsa umminsa ce, najeeb ya karaso ya xauna gefensa yace "y Khaleel Ummi tace tun safe ka ki cin komae" Khaleel bae ce masa komae ba ya dauke kai kawae, Najeeb yyi shiru yana kallon abokin nasa, lkci daya wani tausayinsa ya shigesa, Najeeb ya dafe kansa ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 74...... Bayan kusan minti goma Najeeb ya dago kai yana kallon Khaleel yace "ka kwantar da hnklin ka plss Khaleel, ynxu ma daga gidansu fateema nake" da sauri Khaleel ya mike xaune yana kallonsa abun tausayi yace "pls re yhu serious frnd, ka samu ganinta" Najeeb yace "yes mun hadu but tace baxata iya tsayawa ba kar dad dinta ya dawo ya same mu, ynxu anjima da daddare xan koma" Khaleel ya kamo hannayensa lkci daya hawaye ya cika idonsa yace "pls frnd help me convince her dat I wasn't d one dat wrote dat divorce letter, plss I beg yhu" Rungumesa Najeeb yyi yace "its OK, I will try my vry best frnd nayi maka wnn alkawarin, but nt until u stop does tearz" Khaleel ya dafe kansa bae ce masa komae ba xuciyarsa na masa kuna, mikewa Najeeb yyi ya fita ya karbo abincinsa gun Ummi snn ya dawo ya ajiye masa yace "ga abinci kaci kar ka sa ma kanka wani ciwon Khaleel" Sae da Najeeb yyi da gske snn Khaleel ya ci spoon uku a abincin ya ki cin sauran, Najeeb na kallonsa yace "ko xuwa gobe da nyt sae mu je ka ba Alhaji mukhtar hkuri na tabbatar xae hkura don bn ji ddin xancen da nake ji ba" Khaleel ya mike da kyar yana kallonsa yace "am going no where" yana kai wa nn ya shige bathroom. Karfe takwas da kusan rabi Najeeb ya isa gidansu Ashnaah, mai gadin yyi ynda ta ce masa, ba a dau lkci ba ta fito ts nufi gun Najeeb dake jingine jikin motarsa, ya kafa mata ido har ta karaso ta rungume hannayenta tace "ina jin ka" Najeeb ya dan sauke ajiyar xuciya yace "ki fada min gskya fateema, re yhu happy ynxu da Khaleel ya sake ki" daga kai tayi tana masa mugun kallo tace "wani irin tambaya ce wnn" Najeeb ya dan yi shiru Snn yace "kafin ki ji abinda ke tafe da ni sae kin ban amsa gskya, re yhu happy now dat d both of u re nt togeda" Ashnaah tace "yes am happy, y won't I b happy, I'm vry vry happy coz I've..." Kuka ta fashe da ssae, Najeeb yyi shiru yana kallonta, ta hade kanta da mota ta dinga rusa kuka kmr an aikota, a hnkli Najeeb yace "karya kike fateema, yhu re nt happy, nevertheless I came on behalf of my frnd" dago kai tayi tana kallonsa har lkcn tana hawaye, Najeeb ya dan yi shiru snn yace "ba Khaleel ne ya rubuta maki takardan saki ba," Ashnaah ta tabe baki tace "kwa dae raina ma kanku hnkli ba ni ba" Najeeb yyi murmushi yace "wllh kuwa its a set up, kinsan Wanda yyi rubutun ya sa a drawernsa" Ashnaah tayi shiru tana kallonsa yace "Ameesha, can yhu still remember d day her mum came to c her" Ashnaah sae kallon Najeeb take a dan rikice, ta shiga gyada masa kai tace "ehh na tuna" Najeeb yace "to ita ta sa Ameesha tayi hka don a tunaninta Khaleel ya fi son ki kan Ameesha, ae tuni ya ma saketa ita ma" hawaye kawae Ashnaah take a sanyaye tana kallon Najeeb, ya gyada mata kai a hnkli yace "yes, wllh wllh ba Khaleel ne yyi rubutun nn ba kin ji na rantse maki fateema, ynxu hka yana can bae da lfya, tok to ur parent plss" kuka ssae Ashnaah ke yi ta ma rasa me xata ce masa, yace "shknn ni xan koma, gobe da daddare xan kuma dawowa sae ki fada min ynda kuka yi ae kin gane ko" kae kawae ta gyada masa ya xaga ya shiga motarsa ita kuma ta nufi cikin gida jikinta a sanyaye, to wae ma meyasa ta damu kanta hka bayan tasan ba son shi take ba shi ma ba sonta yake ba. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 75..... Washegari da safe Khaleel na kwance dakin umminsa Rukayya ta shigo wae mai gadi yace wani bako na sallama da shi a waje, ya mike xaune yana kallonta yace "waye?" Tace "ni ma ban sani ba" Khaleel ya dan yi shiru snn yace "Abba ya fita ne" Rukayya tace "ehh tun safe ya fita," ko kadan Khaleel bae son haduwa da dad din nasa, ganin wani irin shasharesa da yake yi tun bayan abinda yyi ma Ameesha, mikewa yyi ya fita don xuwa ganin bakon nasa. Da mmki yake kallon Al-ameen yace "kai ne bako kuma?" Al-ameen yyi murmushi yace "yes ina jin kunyan Ummi ne, na dde ban xo gaisheta ba" Khaleel yace "ae tasan ba garin nn kke aiki ba" Al- ameen yace "na ta kiran nmbrka no answer, shi yasa nace mai gadi yace kayi bako" Khaleel yace "wayar na bedroom dina, ni kuma dakin Ummi nake, mu shiga daga ciki mana" bbu musu Al-ameen ya bi sa har cikin gidan ya gaida Ummi snn suka nufi dakin Khaleel, Al-ameen sae kallon abokin nasa yake ganin ynda ya rame, Khaleel na dan kirkiran murmushi yace "let me get yhu drink" Al-ameen yace "No No am OK wllh" Khaleel ya koma ya xauna yana tambayarsa iyalinsa, Al-ameen yace "they're ol fyn, wai in tambayeka Khaleel" Khaleel yace "OK ina jin ka" Al-ameen yace "na taba maka wani laifi ne duk xaman mu tare?" Khaleel ya wara idonsa yace "laifi kuma na me?" Al-ameen ya girgixa kai yace "na ga ni na damu da kai, kai kam bbu alamar hkn, wae ynxu ace ga abinda ya faru sae a bakin Umar nake ji, shi ma Najeeb ne wae ya gaya masa, wae meyasa ka fi ba ma Najeeb din nn Value ne, ynxu me gayen nn ya tsinana maka throughout life din ka bnda tsiya, I c no reason to b frndin a guy like him, he is worst, wen I say worst I mean worst kai ne baka gane ba har ynxu, dat a side ka gaya min me ya faru, hw manage" Khaleel ya sauke ajiyar xuciya cike da damuwa yace "wllh don't really no where to start frnd, OK kaga ni dae nasan we went to party nd of course without being told I knw I got drunk a can kuma ni bn ce xan sha giya ba Najeeb ne ya kawo min, so at d end dae I found my self at home at early dawn, nd of course I started vommittn coz idan na sha giya over hka yake min, so ina bacci sae Najeeb ya kawo min magunguna ya fada mata ynda xata ban idan na tashi shknn ya tafi, ina tashi kuwa ta shigo xa ta ban maganin to a nn ta ga takardan, kasan Allah Al-ameen ba ni ne na rubuta ba kuma writtin dina ne jikin takardan" a sanyaye ya karashe mgnr, kallonsa kawae Al-ameen yake da mmki, can ya sauke ajiyar xuciya yana murmushi yace "kun taba mgnin saki da wani, misali ko da wasa kace ae xaka saketa ko kuma makamancin hka" Khaleel yace "not at all, nasan Ameesha ce ma, coz ita kadae ta iya rubutuna" Al-ameen yyi murmushi yace "to kafin ka bar gida ranan kae baka lura sa takarda cikin drawern ka ba?" Khaleel yace "a ciki fa na dauki wristwatch dina, I saw nothin inside ae bana barin komae ciki, sae bayan fita na aka sa ka" Al-ameen yace "uhmm meyasa baka xargi Najeeb ba coz ka ce ya shigo ya bada drugs a ajiye maka" Khaleel yace "Najeeb kuma, Haba Haba dats d lst person I will suspect a duniya I knw he can never do dat 2 me" murmushi kawae Al-ameen yake yana kallonsa yana girgixa kai, hkn yasa Khaleel ya dan hade rae. A sanyaye Ashnaah ta karaso falon Abbanta ta durkusa tana kallonsa, Abba ya kalleta yace "ba kiyi bacci ba" tace "uhn ynxu xan yi" Abba yace "to ya aka yi" ta dan yi shiru snn a hnkli ta soma mgna kanta a kasa, "Abba dama wae ashe ba shi ya rubuta wnn takardan ba da na gani abokiyar xama ta ce ta rubuta ta ajiye a dakin don in gani wae, Abba ba shi ya rubuta ba wllh" kmr xata yi kuka ta karashe mgnr, da mugun mmki Abba ke kallonta lkci daya yana murmushi yace "Haba? Ke wa ya gaya maki?" Da sauri ta dago tace "abokinsa ne ya xo ya gaya min, wllh Abba ba shi ne ya rubuta ba" ko kadan bata san lkcn da Abbanta ya mike ba kawae jin saukan wani mari da ya kusan kai ta kasa tayi, ya kuma kai mata wani marin ta mike a gigice tana kwala ihu, da gudu momy ta fito, ita kuma tayi ta kanta, cikin fushi momy tace "meye hka Alhaji me ta maka" Abba yace "wllh wllh in har wancan dabbar yarinyar bata yi hnkli ba a gidan nn sae nayi mugun ba ku mmki dama na lura da take takenta, kuma ko bayan rae na ban yadda ki da ta sake aure ta koma gun matsiyacin nn ba, Neva" cikin tsawa ya karashe mgnr. Yana kai wa nn ya nufi dakinsa. Momy ta juya ta nufi dakinsu Ashnaah ta sameta sae aikin rusa kuka take Ashfah na lallashinta, momy ta hade rae tace "wani xancen kika xo ma da Abbanki?" Cikin kuka tace "momy kin ga fa wae yace ba shi ne ya rubuta takarda...." Tsawan da ya gigita ta momy ta daka Mata tana nuna ta da dan yatsa tace "wllh idan baki kama kan ki kin shiga hnklin ki a gidan nn ba xa ki sha mmki na, don uban ki me kike nufi, ko kin fara hauka ne, to ki kama kan ki, kuma duk me Abban ki xae maki wllh ko a gyalena don ba ke kadae na Haifa ba da xa ki sa min ciwon xuciya, sha sha sha kawae" momy na kai wa nn ta juya ta fice daga dakin. 76..... Washegari da kyar Ashnaah ta iya tashi da asuba don yin sllh, duk jikinta yyi mata nauyi, tana idar da sllh tayi duk abinda tasan take yi snn ta shiga shirin makaranta, a tare suka gama shiryawa da Ashfah snn suka sauko downstairs don yin break, ita dae Ashnaah ko ruwan tea bata sa a bakinta ba tana dae xaune ba, Ashfah da ta fita harkar ta ta mike ta nufi sama don dauko jakar makarantar ta, a sanyaye Ashnaah ta bi bayanta ita ma ta dauko Jakarta, bata bi ta kan babban wayar da Abba ya bata tun shejaranjiya ba nn ta bar sa gaban madubi ta tafi da karamar wayarta kawae. Falo suka nufa don gaida Abbansu da ya fito a lkcn ba tare da ya kallesu ba ya amsa snn ya mika ma Ashfah dubu daya da Dari biyar yace "ki dauki dubu daya ki bata Dari biyar tunda ke ba driver xae kai ki ba" mikewa suka yi suka bar falon bayan sun sallami momy, Ashnaah ta shiga mota a sanyaye suka bar gidan da driver. Karfe biyu saura Ashnaah ta fito daga lecture ta xa ta samu usman da ke jiranta tun bayan sllhr azahar a waje ta hade rae tace "ga ni" ya dan yi shiru snn yace "har kun gama lecture din ne" tace "kmr ya mun ga ba nace maka sae shidda ba yau, kaga usman kawae kana son ja min mgna ne gun Abbana, ynxu idan aka ganmu aka je aka fada masa wani mataki kke tunanin xae dauka a kaina wnn karan, kaga idan har ka san kana so na ni dae ka fita harkata har in gama karatu indae har so na kke, tun da burin Abbanmu knn muyi karatu ni da yar uwata" tana kai wa nn ta daure fuska ta rungume hannayenta, shiru yyi kawae yana kallonta, can bayan kusan minti biyar ya sauke ajiyar xuciya yace "to shknn Fateema, I've heard, Allah sa hkn ne mafi alkhairi i will do as u said, I will wait" sallama yyi mata ya nufi motarsa ta bi sa sa harara tare sa jan tsaki ta bar wajen. Da daddare Ashnaah tayi sneakin ta fito ta samu Najeeb dake jiranta a waje kmr ynda mai gadi ya kirata ya sanar da ita, yana ganinta yyi murmushi yace "welcm, any good news," girgixa masa kai tayi tana kkrin danne kukan da ke neman kubce mata tace "nobody is willing to blive dat, they ol tot it's a lie" kasa daurewa tayi ta fashe da kukan, Najeeb yyi shiru yana kallonta snn a hnkli yace "dama kina son Khaleel ashe Fateema, shine kike kuma neman hanyar da xae sake ki...." Da sauri ta goge hawayenta ta katse sa fuskarta a daure tace "hka nace maka, har shi yana da abun da xa a so shi, kai na kawae nake ji ma da aka mayar dani baxawara at my early age" tana kai wa nn ta juya da sauri ta bar wajen, ya shiga kiranta da sauri amma tuni ta shige gate yace "shit", gidansu Khaleel ya nufa, Khaleel ya mike da sauri ganinsa yace "ya kuka yi" Najeeb yace "no gud news, tsohonta bae saurareta ba hka ma mum din, she was so depressed, cryn cryn" a hnkli Khaleel yace "re yhu serious" Najeeb yace "wllh kuwa, wae ku da kunsan kuna son junanku ku ke ta wani ja ma juna aji aka ki xaman lfya kullum cikin fada ku ke, to ynxu da kuka rasa juna ae kun ga value din junan ku," A sanyaye Khaleel yace "ni ne na kamu da sonta da ddewa but ita nasan bata so na, bna ma gabanta u knw" Najeeb ya xaro ido yace "in ji wa bata sonka, kullum naje bata da aiki sae na kuka, is she just cryn for cryn sake or wat, kuma da bata son ka da wllh baxata saurareni ba bare har ta yi ma iyayenta magana, duk kun kamu da son juna kuna can kuna hauka baku sani ba, nafi ma tausaya mata wllh, don ita yarinya ce ssae gashi xuciyarta xae wahala" dariya Najeeb ke yi har da dafe kai yace "amma so bae ma Khaleel da Fateema adalci ba, ya kai su ya Baro ba tare da sun lura ba" kallonsa kawae Khaleel ke yi har ya gaji don kansa ya daina dariyan, a hnkli Khaleel yace "it seems funny ryt" Najeeb yace "not at all, ynxu ya kke ganin xa ayi kuma, am alwayz dia 2 help yhu frnd" Khaleel ya sauke ajiyar xuciya yace "ganinta kawae nake son yi" Najeeb yace "dats vry simple kawae ka je gidan nasu kayi ma mai gadi mgna nn da nn xae kirata ta fito hka muke yi" a hnkli Khaleel yace "baxa ta fito ba idan ta san nine" Najeeb yace "says hu? Ynda take nemanka ido rufen nn me xae hanata fitowa kawae kai dae ka je, kuma ai ba cewa xaka yi kai bne, kawae Ca xaka yi ayi maka sallama da ita nn take xae kirata kuma xata yi tunanin ni ne ta fito " Khaleel yyi shiru snn ya dafe kansa yace "to Allah yasa ta fito" Najeeb yace "in' sha Allah ma xata fito, kae wae ashe su twin ne baka taba gaya min ba Khaleel" tsaki Khaleel yyi ya mike ya nufi bathroom kawae. Karfe takwas da rabi na dare Khaleel ya isa gidansu Ashnaah, da kyar iya ya fitowa daga motar Najeeb da ya xo da, ya nufi gun mai gadinsu don nesa da gidansu yyi parkin, suka gaisa da mai gadin snn ya gaya masa warce yake nema, mai gadin yace to Bari a kirata, komawa Khaleel yyi ya jingina jikin motarsa xuciyarsa na bugawa, ba a dau lkci ba ta fito da hijab dinta har kasa, a sanyaye take tahowa ya kafa mata ido ganin ynda ta rame duk ta xama kmr ba Ashnaah ba, har ta karaso inda yake bata san ba najeeb bne don bbu haske gun da yyi parkin, ta tsaya dan nesa da shi ta rungume hannayenta tace "gani" 77..... Kasa ce mata komae Khaleel yyi, hkn yasa ta dago kai tana kallonsa, cak taji komae ya tsaya mata tana kallonsa don bata taba tunanin gninsa a lkcn ba, nan da nn ta saka kuka ta juya da sauri xata bar wajen ya rikota da sauri ya rungume ta, kuka ssae take a jikinsa har da shessheka, ya runtse idonsa don bae son jin sautin kukan nata, ganin ba shiru xata yi ba ya sa ya dago kanta a hnkli murya can kasa yace "ni na sa ki kuka koh? Baki son ganina na sani...." Da sauri ta mayar da kanta kirjinsa tana ci gaba da kukanta, a hnkli ta ji yace "am sorry fateema, ni ban sake ki ba, y on earth will I do dat bayan nasan ina son ki y?" Kasa ci gaba yyi sbda tokarewa da muryarsa yyi, da kyar ya iya ci gaba yace "ina son ki fateema blive me, I luv yhu with ol my heart, I luv everything about yhu I knw I can Neva be without yhu, I so luv yhu fateema, I Neva gave yhu a divorce letter yhu re still my wife" kuka ssae Ashnaah take ta ma rasa me xata ce masa, dago kanta ya kuma yi yana kallon kyakkyawan fuskarta da ya wanke da hawaye, shi ma ta ga hawayen a fuskarsa ya sa hannu ya shiga share mata hawayenta yana kallon cikin idonta, amma kmr sake tunxurata yake sae kuka take ssae, lumshe ido yyi ya jawota jikinsa lkci daya ya saka bakinsa cikin nata a hnkli, nn da nn kukan da take ya dauke, ya juyar da ita a hnkli ya jinginar jikin mota ya shiga kissn dinta kmr an aikosa, kasa hanasa tayi ta runtse ido, lkci duk ya kashe masu jiki ganin tana neman sulalewa kasa don kasa daukarta kafafuwanta suka yi yasa yyi saurin dagota ya cire bakinsa a nata ya rungunmeta ssae ita ma hka, sun fi minti biyar a hka idonta a lumshe, a hnkli taji yace "ki tausaya min fateema ki dawo gidana a matsayin matata, in gwada maki irin son da nake maki plss" nn da nn ta fara wani sabon hawayen, da kyar muryarta baya fitowa tace "Abbana baxae yrda ba" ya jinginar da ita jikin mota yana kallon fuskarta ta sunkuyar da kai da sauri, kmr warce ta tuna abu ta xabura da sauri tace "ni xan wuce kar a ga bana gida" bata jira cewarsa ba ta juya da sauri xata bar wajen ya rikota a sanyaye yace "plss ki gaya min inda xan dinga ganin ki" ta daga kai tana kallon idonsa da ya kada yyi ja, ta sunkuyar da kai da sauri, a hnkli tace "sch" bata jira cewarsa ba ta fixge hannunta ta nufi cikin gida da sauri, Khaleel ya fi minti goma a cikin motar ya kasa barin wajen ya hade kai da steering, daga karshe dae yyi karfin hali ya tada motar ya ja ta da kyar ya bar anguwar. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 78..... Washegari da rana Ashnaah na fitowa daga lecture da frnds dinta ta hango motar Khaleel, dauke kai tayi da sauri, tayi kmr bata gansa ba tana ci gaba da tafiyarta kawayenta na biye da ita a baya, khaleel ya bi ta da kallo ya ga ta nufi wani cafeteria ta xauna ta ciro littafinta ta ajiye gabanta su ma duk frnds din nata suka xaxxauna, kasa fitowa yyi daga motar don ba habit dinsa bne bin mace but ya xama dole ya bi fateema, bude motarsa yyi daga karshe ya fito rike da wayarsa ya nufi cafeterian da suke xaune cikin tafiyarsa ta kasaita, da yake duk yawanci an fito daga lecture duk yan mata suka rakasa da kallo tsabar haduwarsa gashi kananan kaya ne jikinsa, ko kadan Ashnaah bata lura da ya fito ya biyota ba, don idonta na kan littafin hannunta duk da hnklinta gaba daya ba kan littafin yake ba, muryar Aisha taji tace "waow waoww kun ga wani hadadden guy, kai wllh wnn yyi ba karya" da sauri Ashnaah ta dago kai don ganin wani guy ne wnn sanin halin Aishan don da wuya ka ji ta ce namiji na da kyau kullum cikin kushe duk saurayin da ta gani take, wani mugun faduwa gaban Ashnaah yyi suna hada ido da Khaleel daga nesan da yake, yyi mata wani mugun kwarjini, bata taba tunanin Khaleel ya kai hka wajen haduwa ba, tasan dae yes he is handsome but bata yi tunanin to this extent ba don Khaleel ya hadu ne ba karya, da kyar Ashnaah ta iya dauke idonta daga kallon da take masa, hka kawae taji ranta ya baci ganin ynda yan Mata ke ta wani kallonsa, wae har da su Ummi abinda ya kuma kular da ita knn, ta sunkuyar da kanta ta hade rae ta ci gaba da kallon littafin gabanta, da kyar Khaleel ya iya karasowa inda suke don shi kansa sae ya ji wani iri ynda ake kallonsa da rana tsaka, Maryam tace "kai gun wa xae xo a nn" Ashnaah dai bata tanka su ba don ranta ya gama baci tunda tasan sun san shi ae, Khaleel ya karaso yana kirkiran murmushi yace "sannun ku ladies" duk suka amsa mashi bnda Ashnaah, kallonsa gaba daya suke da mmki don sae a lkcn suka ganesa, Ummi tace "lah ashe kai ne ina yini" ya amsa da fara'a yana tambayarta ya karatu, Aisha da ta ji kmr ta nutse kasa don kunyan Ashnaah tana sussunkuyar da kai ta gaishesa ya amsa yana mata murmushi, Haba no wonder shi yasa Ashnaah bata tanka su ba, mikewa duk suka yi sbda kunya xa su bar wajen, Khaleel yace "haba ku yi xamanku ni ba dde wa xan yi ba, I will b off soon" Aisha dae taki xama tace xata dauko abu a class ta samu ta bar wajen da sauri, Ummi da Maryam ma cikin dubara suka bar wajen, sae a snn Ashnaah ta dago kai fuskarta a daure sae taga wae duk yan matan wajen kallonsu suke, wasu na gulma, mayar da kanta tayi kan buk dinta don bata son su hada ido da Khaleel da ya kafa mata ido, a hnkli taji yace "ina yini" kasa amsa masa tayi ta dago tana kallonsa suna hada ido ta sauke idonta da sauri, taji yace "u re uncomfortable ryt?" Bata ce komae ba ta kuma kallonsa, murmushinsa mai kyau ya sakar mata murya can kasa yace "me yasa ba ki sa Nikaf ba yau" nan ma bata ce masa komae ba, bae kuma cewa komae ba har na kusan minti takwas, mikewa yyi a hnkli yana kallonta a sanyaye yace "shknn bari in tafi, seems ina damun ki koh Fateema" daga kai tayi tana kallonsa ita ma jikinta yyi sanyi, murmushi yyi mata yace "gobe xan xo" bae jira cewarta ba ya juya da sauri ya bar wajen, mikewa tayi jiki ba kwari ta dauki jakarta ta bi bayan sa, kusan a tare suka iso motarsa, ya juya yana kallonta, bata Bari sun hada ido ba ta xaga ta bude bck seat shiga, shima ya bude seat din bayan ya shiga yana kallonta, da kyar ta iya bude baki tace "ina yini" murmushi kawae yake, hkn yasa ta dago kai ta galla masa harara fuskarta daure, dariya ya shiga yi yana kallon cikin idonta, Ashnaah tayi shiru tana kallonsa a sanyaye don bata taba ganin dariyarsa ba sae wnn vry moment din, lkci daya shima ya daina Dariyar yyi shiru yana kallon cikin nata idon, murmushinta mai kyau tayi lkci daya ta sauke idonta kan long fingers dinta ta shiga wasa da su, bae taba ganin murmushinta ba shima sae wnn vry moment din, a hnkli ya matso kusa da ita ya dago kanta yana kallon kyakkyawan fuskarta, rungunmeta yyi murya can kasa yace "I love yhu wife" lumshe idonta tayi ta daura kanta kan kirjinsa tana shakar kamshinsa me ddi, kmr warce ta tuna abu kuma ta janye jikinta daga nasa tana kkrin bude mota ta fita tace "drivernmu xae xo daukana ynxu" ya rikota da sauri ya marairaice mata yace "plss ki kawo mana solution fateema am lost, nobody is willin to blive me, nt even my parent, ke kadae ce kika yrda da ni" Ashnaah ta sunkuyar da kanta don kar ya ga hawayen idonta da kyar tace "nima ba yrda dani xa ayi ba, gwara mu hkura kawae, dama ae ba son juna muke ba, so wats there don mun rabu..." kuka ta fashe da tana kallonsa, shi kam rasa ma me xae ce mata yyi, dae dae nn drivern gidansu ya iso, Ashnaah ta shiga share hawayenta da sauri ta bude motar ta fice. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 79..... Ashnaah na bude dakinsu bayan ta dawo daga sch ta samu akwatunan ta gaba daya da kayayyakinta a dakin, kayan gado ne kadae bata gani ba, kasa karasawa cikin dakin tayi Ashfah da ke xaune tana ta kwafan note ta kalleta tace "har kin dawo" Ashnaah ta karaso cikin dakin a sanyaye tana ci gaba da kallon kayayyakin tace "waye ya kwaso min kayana" Ashfah tace "ni ma nn na same su" Ashnaah bata ce komae ba jiki ba kwari ta nufi kan gado tayi kwanciyarta kmr me shirin yin bacci don bata son yar uwarta ta lura da halin da ta shiga a lkcn. Har aka kira magrib Ashnaah bata shiga kitchen ba bare ta dauki abincin ta kwata kwata bata da appetite ta rasa me ke mata ddi kawae, Ashfah dae na ta harkar gabanta, da kyar ta mike ta nufi bathroom don yin alwala, tana xaune kan darduma bayan ta idar da sllh momy ta shigo dakin, tana kallonsu tace "waye ya bar min abinci har ynxu a kitchen a ajiye" Ashnaah ta mike tace "na ci abinci a sch ne momy shi yasa bn dauka ba" kallonta kawae momy ke yi, hkn yasa ta sunkuyar da kai momy ta juya ta fice daga dakin, Ashnaah ta mike ta shiga bayi don yin wanka, ana idar da isha Ashfah ts sauka downstairs ta dauko dinner dinta a kitchen ta dawo dakin, Ashnaah ta mike gudun kar momy ta kuma dawowa ita ma ta sauka kasa ta dauko nata abincin a kitchen ta fito, falo ta nufa ta gaida Abbanta dake xaune yana kallon news, bbu yabo bbu fallasa ya amsa ba tare da ya kalleta ba ta mike a sanyaye ta nufi sama rike da abincin ta, tana xaune tayi jigum ta sa abincin a gaba ta kasa ci wayarta da ke gaban madubi ya soma ring, Ashfah da ke kusa da wajen ta juya don dauko mata, da sauri ta mike har tana tuntube ta riga ta dauke wayar, Ashfah ta juya tana kallonta da mmki snn ta tabe baki ta ci gaba da abinda take, Ashnaah ta daga wayar ta kara a kunne bata ce komae ba, can tace "toh" snn ta katse kiran, hada ido suka yi da yar uwartata ta dauke Kai da sauri ita dae Ashfah bata ce komai ba, Ashnaah ta mike cikin dubara ta dauki hijab dinta ta nufi window ta bude ta jefar waje snn ta rufe windon ta nufi kofa rike da cup kmr xata debo ruwa ta fice daga dakin. Kitchen ta nufa Abba ya bi ta da kallo hkn yasa gabanta yyi mugun faduwa ta debo ruwan kawae ta fito ta koma sama ta shiga dakinsu, gefen abincinta ta ajiye ruwan snn ta xauna ta dauki spoon kmr me shirin cin abinci, ta dae jujjuya shinkafar kmr ta ci snn ta kuma mikewa bayan kmr minti biyar ta nufi kofa don kai kwanon kitchen, Satan kallon Abba kawae take har ta shige kitchen ta ga kallonsa kawae yake wnn karan. A hnkli Ashnaah ta bude kofar kitchen dinsu ta fice snn ta kullo ta nufi inda ta jefa hijab dinta ta dauka ta sa, tana waige waige ta fice daga gate. Yana jingine jikin motarsa ta karaso ba tare da ta bari sun hada ido ba tace "ga ni" yyi shiru bae ce komae ba hkn yasa ta daga kai tana kallonsa, yyi mata murmushi a sanyaye yace "tnxx 4 cumin sweetheart" bata ce komae ba ta sunkuyar da kanta, yana kallonta yace "Abba na ciki koh" kai ta gyada masa kawae, yyi shiru snn a hnkli yace "I knw yhu re taking a risk by comin out, forgive me for dat" bata ce komae ba nn ma, ya karaso kusa da ita ya marairaice yace "ina son ganin Abba plss xan iya shiga, I need to tok to him may b he will get me" ta xaro ido a tsorace tana kallonsa tace "A'a bbu ruwana" a hnkli ya dafa shoulders dinta xae yi magana aka bude gate, duk suka juya da sauri barin Ashnaah da xuciyarta ya kusa shigewa cikinta don tsoro, ido hudu tayi da Abbanta, ta fasa ihu a tsorace tana cewa "wayyo na shiga uku na lalace" lkci daya jikinta ya dau rawa. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 80..... Juyawa Abba yyi bae ce komae ba ya koma cikin gida, Ashnaah ta daura hannu a ka ta dinga rusa kuka tana cewa ta shiga uku, kasa ce mata komae Khaleel yyi shima duk jikinsa yyi sanyi, juyawa tayi daga karshe ta nufi cikin gidan da sauri tana ci gaba da rusa kuka, kiranta Khaleel ya shiga yi bata ko waiga ba ta shige gate, ya hade kai da mota xuciyarsa na masa kuna. Kasa karasawa cikin falo Ashnaah tayi har lkcn tana kuka ssae, Abba kam na xaune yana canxa tasha da remote, momy ce ta sauko falon ta shiga kallon Ashnaah da mmki, ganin ynda mai gidan nata ya hade rae yasa ta xauna falon ba tare da ta ce komae ba, shima bae ce mata komae ba sae kallonsa yake, ta gaji da xamanta ta mike ta koma sama har lkcn Ashnaah na tsaye bakin kofar falon, har imaginin din irin abinda Abba xae mata idan ya kamata ta dinga yi, daga karshe da ta gaji da tsayuwa ta sulale nn kasa ta xauna tana ci gaba da kukanta a hnkli, har kusan sha daya tana gun a xaune, Abba ya mike bayan ya gama abinda xae yi ya kashe kayan kallon falon ya rufe laptop dinsa ya nufi sama da shi, Ashnaah ta bi sa da kallo a sanyaye, a takaice dae falo Ashnaah ta kwana ranan a kan carpet don gani take kmr tana shiga daki xae bi ta yyi mata duka, a idonta aka kira sllhn farko har ma da na biyu, tana jin Abba ya sauko don xuwa masallaci ta mike xaune da sauri, har sae da ya fita snn ita ma ta mike da kyar ta nufi bathroom din dake falon don yin alwala, biyar da rabi Abba ya dawo daga masallaci, bae ko kalli inda take ba ya nufi sama. Da safe hka ta dinga kame kame a gidan, gashi momy ma ta hade Mata rae, bbu tantama Abba ya gaya mata abinda ya faru, karfin hali tayi tayi shirin sch duk da tasan Abba ba barinta xae yi ta tafi ba, suka sauko falon a tare da Ashfah don ita ma ta shirya, bakinta na rawa ta gaishesa bae tanka ta ba, ya ciro dubu daya ya mika ma Ashfah yace "Allah ya kiyaye" mikewa tayi tana kallon yar uwarta a sanyaye ta nufi kofa, Ashnaah ta share hawayen da ke neman gangaro mata xata tashi ita ma Abba yace "koma ki xauna" ba musu ta koma ta xauna tana ci gaba da share hawayen fuskarta, Abba ya dauki waya ya kira momy ta sauko ta shigo falon ta xauna, Abba yace "fateema" da kyar Ashnaah ta iya daga kai tana kallon mahaifin nata, hawaye na gangaro mata, Abba yace "baxan maki dole ba kmr ynda na maki a baya duk da ke kika xabar ma kanki hkn wancan lkcn ma, ynxu in kin san kina da Wanda kike so kiyi masa mgna ya turo nn da kwana biyar, bana tunanin xan Bari ki kara sati uku a gidan nn ba tare da na aurar da ke ba, kin fi karfina Fateema, islamiyyar ki bata maki amfani ba a rayuwa, in har Allah yyi xa ki ci gaba da karatu to kya yi a gidan mijinki, just kwana biyar na baki ki fidda miji, snn daga yau har xuwa ran da xan aurar da ke bna son ko bakin wancan kofar ki tsaya bare har ki fita, falo ma ni na hanaki saukowa, tashi ki ban waje" jiri ne kawae ke kwasar Ashnaah daga xaunen da take, momy kam bbu abinda take sae hawaye, da kyar Ashnaah ta iya dafa kujera ta mike har lkcn tana ganin jiri ssae, hka kawae ta nemi kuka ta rasa, ikon Allah kadae ya kai ta daki ta fada kan gado ta runtse ido ko xata ji saukin irin kunar da xuciyarta ke mata. Hka Ashnaah ta kasance tamkar kurma a gidan tun daga ranan ba uhm ba uhm uhm, sae dae tayi ta bin ka da kallo abinci sae ya xamo tamkar makiyinta ko ganinsa bata son yi, kowa ya fita harkarta bnda Ashfah da ke taya ta kuka duk dare don bata da aikin yi a wnn lkcin sae kuka, duk ta rame ta lalace kmr ba Ashnaah ba , ko ya xata runtse ido Khaleel kawae take gani, ta rasa ynda aka yi son Khaleel ya shigeta hka yyi mata irin wnn kamun, duk lkcn da xata yi sllh sae ta roki Allah ya cire mata son Khaleel a xuciyarta gaba daya ta huta, bangaren Khaleel ma hkn take, bashi da aiki sae na tunanin Ashnaah kullum sae ya je sch ace masa bata xo ba duk ya fice hayyacinsa umminsa kadae ke tausayinsa don ko kallonsa dad dinsa baya yi, ko ya je gidansu Ashnaah mai gadi cewa yake Abbanta ya hana a bude mata gate, da ka gansa kasan yana cikin damuwa ssae, kawae shi dae ya ganta ko xae ji sanyi a ransa, gidan smll mum dinsa ya nufa ranan wata Friday da yamma, Meenah na kwance falo abun ta hnkli kwance tana kallo, tana ganinsa ta mike xaune da sauri, ya karaso cikin falon yana kallonta a sanyaye, ya xauna yace "momy fa" da mmki take kallonsa don Khaleel bae taba mata mgnr arxiki ba iya saninta da shi, tace "ta fita" yana kallonta yace "plss wani taimako na xo kiyi min Amina" kallonsa kawae take ta ma rasa me xata ce, don sae take ganin kmr ba Khaleel bne, don ya rame ba kadan ba, can dae tace "ina ji" ya dan marairaice mata yace "its a secret between us pls, gidansu fateema xa ki je min plss kawae ki ganan min ko tana lfya dats ol" Meenah tace "to shknn ka bani address ko gobe sae in je" nn take ya rubuta mata address din ya bata, snn ya bata wani wayarsa yace "ki bata wnn xan kirata" dubu biyar ya bata kudin mota snn yyi mata godiya ya bar gidan. Dat same day Ashnaah na xaune dakinsu ta sa Ashfah gaba sae rusa mata kuka take don ranan ce rana karshe da Abba ya bata ta fidda miji kuma ya turo daga gidansu, Ashfah ma sae taya ta kukan take abun tausayi, da kyar ta iya ce mata to sister ki kira Usman nasan xae amince tunda yana son ki, cikin kuka Ashnaah tace "bana son sa, kuma ni mijina bae sake ni ba" Karfe biyar da rabi Ashnaah ta sauka xuwa falon Abbanta don amsa kiran da yake mata, ta xauna a kasa ta sunkuyar da kanta, Abba yace "na ji shiru ne shi yasa nace a kira min ke" ta fashe da kuka ssae tace "Abba ni bni da wnda zan turo wllh" Abba ya dan yi shiru snn yace "to idan na hada ki da nawa choice din kina ganin na maki adalci don bana son takuraki sae dae fa aure ne dole sae kin yi sa nn da wata daya" kai kawae take gyada masa tana hawaye, Abba yace "kin amince da in maki xabin da nasan baxae cutar da ke ba" da kyar ta iya cewa "na amince Abba" Abba yace "gud tashi ki tafi Allah yyi maki albarka" mikewa tayi ta nufi daki da sauri ta fada kan gado ta dinga rusa kuka kmr ranta zae fita. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 81..... Washegari Saturday Khaleel na dakin Umminsa a kwance Dad dinsa ya shigo fuskar nn tasa a daure yana kallonsa yace "kana ji na, wllh today shud be d 1st nd lst day da xan samu lbrin ka je gidansu yarinyar nn, ni nn na haneka da sake xuwa inda suke, wae shin yarinyar nn yar gwal ce ko me, har ubanta xae kalli tsabar idona da girmata ya gaggaya min mgna, shi din bnxa to wllh ko da ace ba kai kayi sakin nn ba da gske ban amince da ka koma ma yar su ba, don da dukkan alama basu gaji mutunci ba, matsiyata ne, in kuma kana son ganin bacin raina to ka tsallake umarni na Ibrahim" Yana kai wa nn ya juya ya fice daga dakin, Khaleel ya mike xaune ya dafe kansa, Ummi kam rasa ma abun cewa tayi, can ta mike ta fice daga dakin ita ma. Da rana Meenah ta iso gidansu Ashnaah, Momy ce ta bude mata kofa, ta gaisheta da ladabi snn tace Ashnaah take nema, momy ta dan yi shiru snn tace "Ayya sae gashi bata nn kuma" Meenah ta dan yi shiru snn tace "momy xata ji ma ne" momy tace "Zaria ta tafi" Meenah tace "to ki bani nmbrta momy" Momy tace "gskya bbu waya a hannunta" a dan sanyaye Meenah tace "to shknn, ni xan koma, kila in dawo ko gobe" momy tayi mata Allah shi kiyaye snn ta kulle kofar, bata ko kalli Abba da ke xaune falon ba ta nufi sama, don shi ne yace ko kawayenta bae yrda da su shigo gidansa ba. Da yamma momy ta shigo daki tana kallon Ashnaah da ke kwance tace "ki je ana jiran ki a falo Fateema" bata jira cewarta ba ta fice, Ashnaah ta mike da kyar don daurewa kawae take xaxxabi ne ssae jikinta, hijab kawae ta sa ta fito ta sauka xuwa falo, yana xaune shi kadae a falon yana danna wayarsa, ta karaso cikin falon ta xauna ba tare da ta kallesa ba fuskar nn nata a daure, daga kai yyi yana kallonta yace "Fateema ryt?" Tabe baki tayi bata ce komae ba, yace "kina lfya" nn ma bata ce komae ba, murmushi kawae kyakkyawan gayen yyi yana ci gaba da kallonta, Ashnaah dae sae kallo take abunta, can yace "amma kin san ni kuwa Fateema" Ashnaah tace "yes na san ka mana, ko ba Sadeeq ba" murmushi ya kuma yi yace "OK shknn tunda kin gane ni" mikewa yyi yana kallonta yace "xan xo da daddare" bae jira cewarta ba ya nufi kofar fita, Ashnaah ta mike ta ja dogon tsaki ta nufi sama. Karfe takwas da wani abu ya kuma dawowa gidan kmr ynda yace, bbu bata lkci ta sako hijab dinta ta sauka kasa ta gaida Abbanta da ke xaune falo snn ta nufi tsakar gida don yana can yana jiranta kmr ynda Ashfah ta ce mata, kujerar da ke kallon nasa ta ja ta xauna, ya ajiye wayar da yake dannawa yana kallonta yace "duk da ba wani sanin juna muka yi hope xa ki amince da ni, of course wnn hadin iyayenmu ne don bna da ra'ayin auren baxawara, na kasance wanda baya tsallaka mgnr mahaifa duk abinda suke so shi nake so, shi yasa na amince da auran ki, bn san a naki wajen ya yake ba" Ashnaah bata ce komae ba, don wani mugun tsanarsa kawae ke mata yawo a xuciya, ya daga kafada jin bata ce komae ba yace "yaushe kika fita iddah?" Tace "wnn ba matsalarka bace" mikewa yyi yace "OK wnn kuma gskya ne, ni xan koma" Ashnaah ta dake tace "ina neman alfarma daya a gun ka don Allah" ya koma ya xauna snn yace "am ol earz" tana kallonsa tace "Abbana nake son kayi ma mgna ya bar ni in ci gaba da xuwa makaranta don Monday xa mu fara exams" Yace "OK I will do dat" mikewa tayi tace "nagode" snn ta nufi cikin gida yana biye da ita a baya, sama ta nufa shi kuma ya shiga falo gun Abba, bae samu wahalar shawo kan Abba ba, Lkci daya Abba ya amince da batun da Sadeeq ya xo masa da, snn Sadeeq yyi masa gdya ya bar gidan, Ba karamin farin ciki Ashnaah tayi ba da Sadeeq ya kirata yace Abba ya yrda, ko ba komae xata ga Khaleel she knw, don babban dalilinta na son xuwa makaranta knn. Ran Monday a tare suka gama shiri da yar uwarta suka sauko falo, Ashfah kadae Abba ya ba kudin mota, yana kallon Ashnaah yace "bae baki kudin mota bne shi me son ki tafi makarantar" Ashnaah ta sunkuyar da kai tana kkrin mayar da hawayen idonta a hnkli tace "ban tambayesa" Dari biyar Abba ya mika mata, ta mike a sanyaye ta nufi kofa. Ji take kmr ta nufi gidan inna ta gaya mata damuwarta amma tsoron Abba ya hanata hkn, kawae ta nufi sch, ko kadan Ashnaah bata yi abun arxiki a papern ta na physics ba ita kanta ta sani, don gaba daya hnklinta baya jikinta ga wani ciwo da kanta yake ssae, Kawae so take a gama exams din ta fita ko xata ga Khaleel, sha daya saura suka fito daga exam hall, bata bi ta kan frnds dinta dake ta xancen exam ba ta nufi inda ta saba xama ta xauna tana jiran Khaleel. Gajiya tayi da xama har kusan Karfe daya bata ga alamarsa ba, masallaci ta tafi tayi sllhn Azahr ta dawo ta ci gaba da xamanta, duk frnds dinta sun tafi gida sun bar ta don karya tayi masu driver take jira, har kusan La'asar bata ga alamar Khaleel ba ga shi ko nmbrsa bata da bare ta kirasa, hkn yasa ta kifa kanta kan table din gabanta ta shiga rera kuka a hnkli, hka ta dinga xuwa sch kullum da sunan xuwa yin exams ko Allah xae sa ta ga Khaleel amma har ana gobe xa su gama exams ba Khaleel ba alamarsa, hkn yasa ta cikin damuwa ssae yawancin papers dinta ynda aka mika mata hka take submittin dinsa, iyaka ta sa exam nmbrta kawae, da kyar Ashnaah ta mike daga gun da ta saba xama idan ta fito daga exams ganin har biyar ya wuce ranan ma bata ga alamarsa ba, shknn daga gobe baxa ta sake fita ba ta sani, tunanin hkn yasa hawaye mai xafi ya shiga bin kuncinta, kmr a mafarki ta hangi motarsa yyi parkin, still tayi xuciyarta na bugawa tana son tabbatar da shi ne ko ba shi bne, fitowa yyi daga motar ya jingina kmr me jiran wani, duk sae ta ga yyi rama ssae kmr mara lfya, da sauri ta nufi gun motar, har ta karaso bae lura da ita ba ta tsaya gefensa, a sanyaye ta ce "Doctor" ya juya da sauri, ta ji ya sauke ajiyar xuciya lkci daya, murya can kasa yace "am happy I saw yhu Fateema" hawaye ne ya shiga bin kuncinta, ganin xata ja ma kanta attention yasa ta bude front seat ta shige ta shiga rusa kuka, Khaleel ya shiga motar shi ma a sanyaye ya dafe kansa, ganin ba shiru xata yi ba yasa ya dago yana kallonta ya jawota jikinsa a hnkli ya shiga rarrashinta, da kyar ta tsaida kukan nata, a hnkli tace "aure Abbana xae min" dago kanta yyi da sauri a rikice yace "wat?" Gyada masa kae kawae tayi hawaye na bin kuncinta, innalillahi kawae yake furtawa, hkn yasa ta fashe da kuka ssae, maimakon ya lallasheta sae shima ya fara hawayen, da kyar ya rungunmeta amma ya rasa da wani kalman xae lallasheta, hkn yasa ya tada motar kawae yyi reverse, da sauri ta tsagaita kukanta tace "ina xaka kai ni" bae tanka ta ba har suka fice daga sch din. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 82..... A hnkli Ashnaah ta tsaida kukan da take tana kallon Khaleel a sanyaye, bae ce komae ba sae drivin kawae yake, ko ba a gaya mata ba tasan inda xa su ganin hanyar da ya dauka, tafiyar kusan minti ashirin suka yi suka iso gida, ita dae gabanta sae faduwa yake barin da ta ga garin da alamar hadari, horn yyi mai gadi ya fito da sauri ya bude masa gate, tsayawa yyi suka gaisa don har ya manta rabonsa da gidan snn ya ja motar ya shiga gidan, yana gama parkin ya juya yana kallon Ashnaah da ke kallonsa har lkcn fuskarta bayyane da alamar tsoro, ya sauke ajiyar xuciya a sanyaye yace "didn't I do the ryt thing?" Ashnaah ta sunkuyar da kai a hnkli tace "yhu re makin me disobey my dad once again" dago kai tayi hawaye na saukowa idonta a sanyaye tace "ka mayar da ni gida plss" Khaleel ya jinginar da kansa jikin kujerar motar ya runtse ido xuciyarsa na tafarfasa, lkci daya ya bude idon da ya kada ssae ya jawota yana kallonta yace "ya kike son in yi fateema, tell me plsss" Ashnaah bata ce komae ba sae hawayen da take, ya bude motar ya fito ya xaga ta inda take ya bude ya kama hannunta yana kallonta kan yace komae ta fito a hnkli, ya sakar Mata murmushi a sanyaye ya rufe motar snn ya nufi cikin gida yana rike da ita. Falo suka xauna Ashnaah dae duk a takure take kmr ranan suka saba xama gida daya da shi, ga wani faduwa da gabanta yake idan ta tuna Abbanta, duk ya lura da ynda ta takura hkn yasa ya mike daga kusa da ita ya koma one sitter ya xauna, ta daga kai tana kallonsa yyi mata murmushi yace "kina jin yunwa koh?" Bata ce komae ba ya mike ya dauki car key yace "bari in Samar maki abinda xa ki ci" da kyar ta iya bude baki tace "A'a ka mayar da ni gida tsoro nake ji" kmr xata yi kuka ta karashe mgnr, ya gyada mata kai a sanyaye yace "I knw, let me get yhu something to eat first" bata ce komae ba ya juya ya fice daga falon ta bi sa da kallo, a hnkli ta shiga bin ko ina na falon da kallo kmr ranan ce ta farko da ta taba shigowa, komae na nn ynda yake sae dae kura da falon yyi, mikewa tayi a Sanyaye ta cire hijab din jikinta ta ajiye snn ta nufi kitchen ta dauko broom don tsaftace gidan, tana ta goge goge da share share Khaleel ya dawo, ajiye ledan hannunsa yyi ya karaso inda take a duke shi ma ya duka yace "sbda me kike ba ma kanki wahala Fateema, its of no need ba xama xa muyi ba ae" bata ce masa komae ba sae mopping dinta take, yace "to shknn let me help yhu" nn ma bata ce masa komae ba ya shiga taimaka mata, a tare suka gyara ko ina na falon tamkar sun dawo ne da xama, ko ina ya dawo fes sae kyalli falon yake, duk sae taji ta gaji ssae don dama manejin kanta take tasan bata jin ddi, da kansa ya nufi kitchen ya wanke plates da cup snn ya dawo falon ya shiga juye mata abincin da ya siyo a take away, kallonsa kawae Ashnaah take sae take ga kmr ba Khaleel din da ta sani bane, dago kai yyi yana kallonta bayan ya gama juye abincin, ganin ynda take kallonsa ya sa ya sakar Mata murmushi, boye fuskarta tayi da tafin hannunta da sauri, ya sauko da ita daga kan kujerar da take xaune yace "gashi na xuba maki" kallon shinkafar kawae take, ya dauki spoon ya diba ya kai mata bakinta, bude bakin tayi a hnkli ya xuba mata shinkafar yana kallon cikin idonta, ta lumshe idon kawae tana tauna shinkafar a hnkli, murmushi yyi yana ci gaba da kallon kyakkyawan fuskarta, da kansa ya dinga bata abincin a baki tana karba har don kanta tace ta koshi, snn ya xuba drink xae bata, kan ya dauka tayi saurin dauka ta kai bakinta, kallonta kawae yake har ta sha rabi ta ajiye ta shiga goge bakinta, har ta manta yaushe rabon ta ci abinci hka ta koshi, sauran abincin da ta rage ya shiga ci, Ashnaah tayi shiru sae kallonsa take, jawota jikinsa yyi tayi lamo, ya daura fuskarsa kan dankwalin da ke daure kanta yana shakar kamshin gashinta, suna nn xaune a hka har aka kira Magrib, Ashnaah ta janye jikinta daga nasa ta mike tsaye da sauri a rikice tace "ka mayar da ni gida plss" mikewa yyi a sanyaye yace "OK let me pray," bae jira cewarta ba ya nufi bathroom da ke falon, komawa tayi ta xauna a sanyaye hawaye cike idonta tana tuna moments dinta a gidan nn, yana fitowa yace mata ya tafi masallaci snn ya fita, yana fita da minti biyar taji alamar an fara yayyafi, mikewa tayi a sanyaye ita ma tayi alwalan ta fito ta tada sllh nn falon, ko da ta idar ruwa ake yi ssae, hankalinta yyi mugun tashi to yau ya xata yi da Abbanta, tana cikin wnn tunanin Khaleel ya shigo gidan, Ashnaah ta mike da sauri ta nufe sa da damuwa tace "lah, ka shiga ruwa ne? Me yasa baka jira aka gama ba?" 83.... Khaleel bae ce mata komae ba sae kallonta yake, ta karaso gabansa ta shiga balle masa buttons din farar shirt din jikinsa ba tare da tayi wani tunani ba ganin ynda ya jike, Khaleel bae ce Mata komae ba sae kallonta yake har ta gama balle buttons din ta cire shirt din daga jikinsa faffadan kirjinsa ya bayyana cikin singlet din jikinsa, da sauri ta juya masa baya kmr warce ta tuno abu da ka ganta kasan ba karamin tsorata tayi ba, Khaleel yyi murmushi ya nufi sama Ashnaah ts bi sa da kallo gabanta na ci gaba da faduwa, ta kusa minti goma a tsaye bata ga Khaleel ya sakko ba, hnklinta gaba daya yyi gida barin ynda ake ruwan nn tasan for sure ynxu ana nemanta, tuna wayarta tayi ta nufi jakarta da sauri gabanta na faduwar mis cals nawa xata gani na momynta don wayar a cylnt yake, mis cal din Ashfah uku kawae ta gani, jikinta na rawa ta shiga kiranta, bugu biyu ta dauka, Ashfah tace "sister wae kina gidan inna ne?" Ashnaah ta fara kalle kallen falon kmr me tsoron Ashfah xata gane inda take in tace ehh, da sauri tace "ehh me ya faru?" Ashfah tace "dama na gaya ma momy" Ashnaah ta dan sauke ajiyar xuciya tace "Abba fa?" Ashfah tace "ya tafi Abuja wae daxu, gobe xae dawo" Ashnaah ta kuma sauke ajiyar xuciya snn a hnkli tace "ana gama ruwa xan dawo ynxu" nn suka yi sallama da yar uwartata snn ta katse kiran ta juya tana kallon sama ganin Khaleel bae sauko ba, cire wayar tayi a cylnt ta mayar jakarta snn ta nufi sama, xaune ta samesa a bedroom dinsa yana xaune gefen gado bayan ya gyara gadon ya dafe kansa, har lkcn singlet ne jikinsa, Ashnaah ta karaso da sauri ta xauna gefensa ta dafa sa tace "me ya faru, kan ka na ciwo ne" bae tanka ta ba, ta Mike ta kashe Ac din dakin ganin har lkcn bae cire kayan jikinsa ba, ta dawo ta kuma xaunawa gefensa da damuwa tace "to ka cire kayan mana kar kayi mura" a hnkli ya dago kai yana kallonta da idanuwansa da suka yi ja, nan da nn hnklinta ya tashi kmr xata yi kuka tace "baka da lfya ne" girgixa mata kai yyi ya rungumota ya lumshe ido, lamo tayi jikinsa gabanta na faduwa, ganin bae ce komae ba yasa a hnkli tace "ka kai ni gida doctor plss dare yyi" dai dai nn aka yi interrupting power, duhu ya xiyarci ko ina na dakin, bbu abinda ake ji sae karan saukan ruwan sama, Ashnaah da gabanta ya fadi ssae ta shiga janye jikinta daga nasa amma ya ki saketa, da kyar muryarta baya fitowa a dan tsorace tace "ka ga an dauke wuta ka kai ni gida don Allah kar Abbana....." Kawae jin bakinsa tayi cikin nata, ta sakar masa kuka a tsorace tana neman kwace kanta amma ta kasa sbda irin rikon da yyi mata, kissn dinta kawae yake lkci daya ya cire dankwalin kanta yana shafa gashin kanta, turasa kawae Ashnaah take tana kuka a tsorace amma yaki kyaleta, ssae Khaleel ya shiga mata abubuwan da yasan nn take xa su kashe Mata jiki, ai ko cikin dan kankanin lkci ya ji ta tsit, romancin dinta kawae yake, cikin dubara ya raba ta da duk kayan jikinta, sae a snn hnklinta ya dawo jikinta da sauri, a gigice ta rikesa tace "na shiga uku me xaka min don Allah doctor ka rufa min asiri ka bari" cikin kuka ssae take magiyan, da kyar Khaleel ya iya ce mata plss wife, girgixa masa kai kawae take a rikice tana kkrin mikewa tana cewa bata so, ganin wahala kawae xata basa don bae ga alamar xata sauraresa ba yasa ya dannneta, kokuwa ta shiga yi da shi tana kwala ihu, amma ta kasa kwace kanta, bbu irin rokon da bata masa ba daren nn amma bae saurareta ba, bae ma san tana yi ba, tana ji tana gani Khaleel ya rabata da pride dinta ta karfi, tayi kukan tayi kukan har ta ji bata iya kukan kuma tsabar wahala, Khaleel bae kyaleta ba sae da ya ga bata motsin kirki ya, dagota yyi da kyar bayan kusan minti uku ya kankameta jikinsa, lkci daya hawaye na saukowa idonsa. Hummm I dedicate dis page to yhu Anty Nafee, Lol kar kuma ki ce min komae ehe. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 84/85 Khaleel ya runtse ido ya kuma kiran sunanta murya can kasa, har lkcn yana rungume da ita jikinsa, jin bata amsa ba sae kukan da take da dashasshiyar muryarta ya sa ya kwantar da ita da kyar ya koma can karshen gado ya xauna tare da dafe kansa yana furta innalillahi wa inna ilaihi raji'un, lkci daya yana da ya sanin abinda ya aikata mata, ssae jikinsa yyi sanyi, ya kusa minti takwas a hka snn ya mike da kyar ya nufi bathroom, ba a dau lkci ba ya fito ya nufi kan gadon a sanyaye, har lkcn bbu abinda take sae aikin kukan da bbu sautin kirki tsabar wahala, ita kadae tasan abinda take ji a wnn lkcn, dagota yyi ta turasa da sauran karfinta ta fashe da wani matsanancin kukan har da sheshsheka, xaunawa yyi gefen gadon a sanyaye yace "kiyi hkuri fateema, forgive me plss, it wasn't intentional" Ashnaah bata tanka sa ba sae kuka take ssae, mikewa yyi xae kuma dagota ta fasa wani ihu da muryarta da bae fitowa, dai dai nn aka yi restoring power, haske ya gauraye ko ina na dakin, da sauri ta shige cikin bargo ta rufe jikinta gaba daya har kanta, Khaleel ya hau gadon ya xauna ya kuma dagota a hnkli yace "let me help yhu plss, u re in pain" kin bari ya cire bargon tayi, hkn yasa ya fixge bargon ta rufe fuskarta a kirjinsa ta rungumesa cikin kuka take cewa "don Allah ka kashe wutan plss" mikewa yyi, yyi ynda tace snn ya dawo ya kuma dagota fadawa jikinsa tayi tana kuka ssae tace "ka kai ni gida don Allah ina rokon ka" daukarta yyi ya nufi bathroom da ita, daren nn Ashnaah ta ga wahala, gani tayi kmr mutuwa xata yi tsabar axaban da take ji, sae da Khaleel ya tabbatar ta ji ruwan xafi ssae snn ya fito da ita daga bathroom din ya kwantar da ita kan gado bayan ya yaye xanin gadon, bbu irin rarrashin da bae mata ba amma kmr da da tunxurata yake, hkn yasa ya kyaleta ya mike jiki ba kwari ya shiga bathroom don yin wanka, ko da ya fito tsit yake jin ta ko ba a gaya masa ba yasan bacci tayi, ya karasa gadon a hnkli ya xauna tare da kunna bedside lamp yana kallonta, ssae ta basa tausayi ganin ynda tayi laushi, amma ya ji tsoron taba ta kar ta tashi, kashe wutan yyi ya kwanta kusa da ita ya jawota jikinsa a hnkli, har bayan minti talatin Khaleel ya nemi bacci ya rasa, wani sabon son Ashnaah ne kawae ke shigarsa, ji yake kmr ta dawo gidansa ne na har abada bbu me rabasu, har dare ya tsala idonsa biyu, iynxu kam ruwan ya tsagaita gaba daya garin yyi sanyi ssae, a hnkli ya ji jikinta ya fara daukan xafi yana rungume da ita, kafin wani lkci jikinta yyi xafi ssae, tunanin wani irin taimako xae mata ba tare da ta tashi ba ya shiga yi, yaga bbu irin wnn taimakon, its either ya bata magani ko yyi mata allura kuma dole sae idonta biyu, kyaleta kawae yyi don baya son jin kukanta kuma, can wajen Karfe biyu ya ji ta fara motsi tana kkrin kwace kanta daga rungumar da yyi mata, ya sake ta a hnkli ta xame daga jikinsa ta koma can karshen gado ta kwanta, bayan kmr minti goma ya ga ta mike xaune tare da hade kanta da gwiwa, kallonta kawae yake cikin duhun, can yaga ta sauke kafafunta kasa alamar tashi xata yi, tana mikewa ta saki wani kara ta durkushe kasa, mikewa yyi da sauri ya nufi inda take yace "me ya faru" a hnkli ta soma rera kuka, ya dagota yace "ina xa ki" cikin kuka tace "xan yi fitsari ne" daukarta yyi ya shiga bathroom din da ita, ganin ba yi xata yi ba yana tsaye yasa ya fita daga bayin, kasa fitowa tayi bayan ta gama don ji tayi kmr ana tsikara mata allura idan ta daga kafarta, kukan ma ynxu yin shi kawae take ba hawaye, da kansa ya xo ya dauketa suka koma dakin snn yyi mata allura guda biyu da kyar don ta bashi wahala, ta dae gama koke kokenta bacci ya dauketa wajen Karfe uku, Khaleel na shigowa falo daga mosque da asuba ya ji wayar Ashnaah da ke cikin jakarta kan kujera ya soma ring, ya kalli agogo ya ga Karfe biyar da minti arba'in, daukar wayar yyi yana kallon screen din ya ga Momy a rubuce, da kmr ya ajiye wayar sae kuma ya fasa yana rike da wayar har ya katse snn ya haura sama a dan sanyaye, bedroom dinsa ya shiga ya kunna wuta, yana kallon Ashnaah, bacci kawae take amma da ganinta kasan she is in pain, ya karasa kan gadon cike da tausayinta yana kallonta, wayarta da ke hannunsa ya fara ring kuma, a tsorace Ashnaah ta farka ta mike xaune da sauri ba tare da ta bari sun hada ido ba muryarta a dashe tace "ina wayar" mika mata wayar yyi ta karba tana kallon screen din, ba karamin tsoro ne ya bayyana a fuskarta ba ganin momynta ce me kiran, bbu wani tunani ta daga kiran ta kara kunne da sauri, fada momy ta soma yi daga daya bangaren tana cewa "wato magana kike son jawo min gun Abbanku ko Ashnaah, da wa ku ka yi xa ki gidan inna ne wae bare har ki kwana, kuma ma ba Abbanku ya hana ki xuwa ba, to maxa gari na wayewa ki dawo gida don ba ruwana yana hanya" momy na kai wa nn ta katse kiran, Ashnaah ta ajiye wayar ba tare da ta kalli Khaleel ba ta shiga kkrin sauka daga kan gadon, ihu ta saki ta koma kasa da sauri ta xauna, sae ga hawaye, shknn ta shiga uku ya xa ta koma gida ynxu, Khaleel ya cuceta, hawaye kawae take bbu sautin kuka, Khaleel ya dawo kusa da ita ya dagota a hnkli ya nufi bathroom da ita, wahalar da ta fi na cikin dare ta kuma sha wnn karan, tsabar kuka har idonta ya kumbura, shi ma ya ji kmr ya taya ta kukan sbda tausayi, yasan ya ji mata ciwo ssae gashi taki bari ya dubata, bbu abinda take cewa sae ita dae ya kai ta gida, da kyar ta dan sha tea ya bata magunguna, duk da irin baccin da take ji damunsa kawae take ya kai ta gida momy na jiranta, inda Allah ya taimaketa ma da rana xa suyi lst paper dinsu na ranan, tara saura Khaleel ya dauketa ya kai ta mota duk da taso daurewa ta taka da kanta amma bae bari ba, har suka iso gidansu bacci take, Khaleel da ya rasa me ke masa ddi a duniyar don gaba daya he is lost ya juya yana kallonta a sanyaye, tashinta ya shiga yi, ta farka da sauri ganin inda suke yasa ta shiga kkrin bude motar xata fita, rikota yyi hawaye cike idonsa yace "Fateema I can't do without yhu, help me plss nd bring out a solution for d both of us, in kin tafi ynxu ban san inda xan kuma ganin ki ba" nn da nn ita ma hawayen ya cika idonta amma ta ki Bari su hada ido, duk da irin haushinsa da take ji sae ta samu kanta da cewa "xan je sch anjima ae" tana fadin hka ta bude motar, ya kuma kamo hannunta a hnkli yace "plss ki dinga shiga ruwan xafi a kai a kai don ki warke kin ji wife, kin dae ga ynda nake maki" da sauri ta fixge hannunta ta fice daga motar, dingishi kawae take shi ma da kyar don ita kadae tasan me take ji, Khaleel ya bi ta da kallo cike da tausayinta har ta shige gate dinsu, dafe kansa yyi hawaye na sauko masa, ynxu da suna tare meye baxae mata ba har ta ji sauki, amma gashi ynxu shi da matarsa bbu daman taimakonta. Ashnaah na shiga compound dinsu ta ga motar Abbanta gabanta yyi mugun faduwa don tasan da motarsa yake xuwa Abuja, kaddae har ya dawo, da kyar tana tafe tana hutawa ta shiga falonsu, yana xaune falo yana waya, xuciyarta ya kusa shigewa cikinta don tsoro, ta karaso cikin falon ta durkusa ta gaishesa a hnkli, ya gyada mata kai kawae fuskar nn tasa a murtuke, juyawa tayi ta gaida momy da ke xaune ita ma tana kallonta ganin ynda idon yar tata ya kumbura, ko ba a fadi ba tasan tayi kuka, a sanyaye ta amsa mata snn ta tambayeta inna, da kyar Ashnaah tace "tana lfya" momy bata kuma cewa komae ba don ita ma karya tayi ma Abba tace da sassafe ta tafi ba kwana tayi ba a can, mikewa Ashnaah tayi tana tunanin ynda xata yi tafiya ba tare da iyayenta sun lura da komae ba, ta runtse ido ta fara tafiya ba tare da ta yi dingishi ko kadan ba, da kyar ta haura sama ta shige bedroom dinsu, ta durkushe kasa ta shiga kukan axaban da take ji tana yarfe hannu, daga skirt dinta tayi jin danshi danshi da abu na saukowa kafarta, tana dubawa taga jini kmr me period, da rarrafe ta nufi bathroom sae da ta ci kukanta ssae snn ta shiga gyara jikinta, ta hada ruwan xafi kmr ynda yace mata ta shiga, ba karamin daurewa tayi ba duk da ba wani xafi gare ruwan ba, snn ta kuma fitowa da rarrafe ta hau gado ta kwanta, nn da nn bacci ya dauketa, Ashfah ce ta tasheta sha biyu saura ta ji jikin yar uwartata xafi kmr garwashi. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 86.... Mikewa xaune Ashnaah tayi da sauri tana kallon agogo tace "har twelve yyi ina da exams Karfe biyu" kallonta kawae Ashfah ke yi da damuwa tace "baki da lfya ne sister?" Ashnaah ta girgixa mata kai da sauri tace "lfya ta lau" bata jira cewar Ashfah ba ta shiga kkrin mikewa da sauri, gaba daya ta manta da lalurar ta, ta fara tafiya tayi still da sauri jin xafi, komawa tayi a hnkli ta xauna don bata son yar uwarta ta fahimce komae, Ashfah tace "ba bayi xa ki shiga ba" Ashnaah tace "da sauran lkci ae" Ashfah bata kuma cewa komae ba ta mike ta nufi kofa ta fita, Ashnaah ta sulalo kasan gadon ta xauna a hnkli hawaye na bin kuncinta, me yasa Khaleel xae mata hka, tuna ko tausaya mata bae yi jiya ba yasa ta fashe da kuka cike da jin haushinsa, tana cikin kuka momy ta shigo dakin Ashfah na biye da ita, da sauri ta shiga goge hawayen fuskarta duk da sun hada ido da ita, tasan Ashfah ce ta je ta kirata, momy ta karaso kusa da ita tana kallonta tace "baki da lfya ne Ashnaah" girgixa mata kai kawae tayi a hnkli tace "period dina ne xae xo shine cikina ke damuna" momy tace "to bari a siyo maki magani, Ashfah dauko mata abincinta a kitchen" Ashfah ta kawo mata abincin, momy kuma ta kai ma driver kudi ya je pharmacy ya siyo mata magani, da kyar Ashnaah ke tura shinkafar gabanta ganin momynta xaune kusa da ita, tausayi kawae take ba uwartata amma bbu ynda ta iya da mijinta shi yasa take yin shiru, tunanin ynda xata mike ta kai plate din abincin kitchen Ashnaah ta dinga yi gabanta na faduwa, momy ta mike ganin ta gama ta dauki plate din tace "ki shirya kafin a kawo maganin tunda kuna da exams" Ashnaah tace "to" momy na fita ta nufi bathroom tana dinginshi, wanka tayi snn tayi ynda Khaleel ya ce mata ta fito daure da tawul, cikin minti goma ta gama shiryawa Ashfah ta shigo mata da magani ta karba ta faki idonta ta jefa jakarta ta sha paracetamol snn ta sa hijab ta shiga sauka kasa a hnkli, gabanta ya fadi ganin Abba xaune falo kuma idonsa a kanta, kasa daurewa tayi duk da ynda ta so dai daita tafiyarta sae da ta yi dingishin nn, bin ta da kallo yyi yace "me ya sami kafar?" Ta sunkuyar da kanta da sauri tace "bugewa nayi jiya" Abba yace "Allah ya sauwake" kasa amsawa tayi don ji tayi she felt guilty inside her, Abba yasa driver ya kai ta sch din, ga mmkinta sae ta ga motar Khaleel a Parke a parkin space din dept din, tana tsaye har drivernsu ya juya, snn ta kuma kallon motar Khaleel, fitowa yyi ya karaso inda take da sauri yace "ya jikin fateema, I was so worried ga shi bbu wayar da xan kira ki" dauke kanta tayi fuskarta a daure ta nufi class da sauri, kiranta ya shiga yi ta sharesa, ya bi ta da kallo a sanyaye har ta bace masa, juyawa yyi jiki ba kwari ya koma motarsa ya hade kai da steering, har aka raba paper Ashnaah hnklinta baya class din, ita bata ma san subject din da xa suyi ranan ba, ko kadan ita kanta bata ji ddin abinda tayi ma Khaleel ba, hnklinta ya ki kwanciya Allah Allah kawae take taje ta samesa kar ya wuce, exm nmbrta kawae ta rubuta masu ta ajiye pen, Maryam da ke gabanta ta lura bata rubuta komae ba ta shiga daga mata cikin dubara don ta kwafi nata amma Ashnaah tayi kmr bata san da ita take ba, lkcn fara submit na yi ta mike da sauri ta bada papernta bayan tayi sign ta fice daga class din, ita ce first din fita ma, fashewa da kuka tayi ssae ganin bata ga motarsa ba a gun da ta barsa daxu, shknn gashi daga yau tasan baxata sake fitowa ba, ganin xata jawo ma kanta attention yasa ta nufi inda ta Saba xama da sauri ta xauna ta kife kanta da table ta dinga kuka, har lkcn la'asar yyi bata ga ya dawo ba, ta nufi masallaci a sanyaye tayi sallah ta dawo, hudu da rabi ta hango motarsa ta mike da sauri, har ya fito yyi irin tsayuwar da ya saba jikin motar da ganinsa kasan baya hayyacinsa, a sanyaye ta nufi inda yake, lkci daya ya hangota ya kafa mata ido ganin ynda take tafiyar har ta karaso inda yake, kasa kallonsa tayi ta sunkuyar da kanta, shima ya kasa cewa komae sae kallonta yake a sanyaye, a hnkli ta bude bayan motar ta shiga, shima ya shiga ya rufe snn ya juya yana kallonta yace "ya jikin" gyada masa kai kawae tayi, ya dago knta yana kallon fuskarta, a hnkli yana kallon cikin idonta yace "kin yadda dani fateema?" Shiru tayi bata ce masa komae ba, murya can kasa yace "if yes ki bi ni duk inda xa ni mu tafi, we shud b far frm home to start a new life wife, I promise to always b there for yhu....." Kuka ne ya ci karfinta don da a hnkli take yi dama tana kallonsa a sanyaye tace "no i can't, hakkin parent dina xae bi ni, nd I will knw no happiness til d end of my life..." Hawaye shi ma ya shiga yi a hnkli yace "ba ki so na knn Fateema" cikin kuka tace "ina sonka amma iyayena fa, tun tasowa na nake disobeying dinsu, no no I can't plss" fadawa jikinsa tayi tana kuka me taba xuciya, ya rungunmeta shima yana hawayen ssae, da kyar ya iya bude baki yace "to ya kike son muyi fateema, my parent re also angry wit me, I lost my job becos of ol dis, ya kike son mu yi plss" kuka kawae Ashnaah take a jikinsa, muryarta na rawa tace "think of another solution plss" . ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 87..... Khaleel ya rungunmeta ssae ya runtse ido yace "am lost wife, I have no idea of any solution" Ashnaah tayi lamo jikinsa bata ce komae ba hawaye na bin kuncin ta, ganin bae kuma cewa komae ba yasa a hnkli tace "in 3wks tym...." Kasa ci gaba tayi ta fashe da kuka, Khaleel bae ce komae ba har lkcn idonsa a runtse, xuciyarsa na masa kuna, tunanin ynda xata dauki xancen da yake shirin fadi mata ynxu kawae yake, ya bude ido a hnkli da nufin gaya mata abinda ke xuciyarsa amma ya kasa, hw on earth xae iya bude baki yace mata xae yi sue din Abbanta, girgixa kai yyi a xuciyarsa yace No, waige waige Ashnaah ta soma ganin kmr motar gidansu ta gani, ae ko taga drivernsu ne, tana kallon Khaleel a tsorace tace "drivernmu ya xo xan tafi" kasa cewa komae Khaleel yyi, hkn yasa ta shiga kkrin bude motar, ya kamo hannunta a hnkli, sunkuyar da kanta tayi, ya ciro wayarsa daya ya mika mata murya can kasa yace "xan kira ki" kai ta gyada masa ta karba xata fita ya kuma kamo hannunta da damuwa yace "kina shiga ruwan xafi koh" sunkuyar da kanta tayi da sauri ta ki cewa komae, ya jawota jikinsa a hnkli yace "tok mana wife" gyada masa kai tayi ba tare da ta kallesa ba don sae taji mugun kunyarsa take ji, yace "da sauki ae ynxu koh" nn ma ta gyada masa kai tayi kawae, ya dauko wani leda da ke dauke da magunguna da dettol ya mika mata snn ya nuna mata ynda xata sha magungunan, Ashnaah bata bari suka hada ido ba ta bude motar ta fice da sauri. Bin ta yyi da kallo yana murmushi har ta shiga motar gidansu, jinginar da kansa yyi a hnkli jikin kujerar motar tare da lumshe idonsa yana tunanin yaushe wnn dramatic play din xae kare a bashi matarsa, Najeeb ne ya fado masa ya mike xaune da sauri, wayarsa ya ciro ya shiga neman layinsa bugu daya ya dauka, Khaleel yace "amma ka ban mmki Najeeb, dama a frnd indeed is nt a frnd in need ban sani ba, yhu just ignored me dis dayz sbda kaga ina cikin matsala koh, Bravo." Khaleel na kai wa nn ya katse kiran, ko minti biyu ba ayi ba Najeeb ya kuma kiransa, "Haba ya xaka ce hka Khaleel, I helped yhu get to her kuma kace nayi ignoring dinka, hu convinced her dat yhu weren't d one dat wrote d divorce content, I've being tryn reachin ur lines for a while ynxu bna samu, kuma ni baka kirani kace ga ynda ku ka yi ba da kaje ranan, dat was y ka ga hka, but mu hadu a gida ltr" katse kiran Khaleel yyi ya mayar da wayar cikin aljihunsa snn ya fito daga bayan motar ya koma driver seat ya tada motar yyi reverse ya bar wajen. Ashnaah na isa gida tun kan ta shiga ta dinga jin muryar inna a falo, ddi ta ji har cikin ranta, ta nufi cikin falon tana murmushi, hararanta Abba ya shiga yi ta sunkuyar da kai da sauri har xata bar wajen inna tace "ina xa ki kuma taho dama ke nake jira" Ashnaah ta karasa a sanyaye ta xauna, inna tace "ashe wae auren ki ya mutu har ana shirin maki wani don an rainani sae ynxu wnn mutumin ke gaya min," Ashnaah dae bata ce komai ba, inna da har ta soma kwalla tace "ni dama Adamu bae mayar da ni a bakin komai ba, yin abinsa yake kai tsaye kmr shi ya haifo kansa, tunda ubansa ya rasu mu ke a hka, wae ace ina raye a maki aure a ki nuna min gida a wani ce min kasar waje aka kai ki, to Akwae Allah, amma a ina kuka hadu da wnn da ya sake ki don baki taba kai shi ya gaida ni ba, shi dan uban waye da xae walakanta mana ke hka" Abba yace "duk wnn ba shi bne inna, magana ya Riga da ya wuce tunda nn da sati uku ne bikinta" Inna tace "yi min shiru malam, idan nace baxa ayi ba wllh bbu me yi aikin bnxa kawae, akuya ce yar aka ce maka halan, ita khadija uban meyasa take xaune har ynxu baka aurar da ita ba, sae wnn da ka tsana ko," Abba yace "ita khadija tana jin maganata baba, wae abun takaicin ma xuwa tsohon mijin nata ke yi kusan kullum wae shi bae saketa ba bayan ga takarda kuma duk iyayensa sun shaida rubutun sa ne, snn wnn yar da bata jin magana sae ta saci hanya ta fita ta samesa suna tadi a waje, to kice baxan kuma aurar da ita ba baba, ae ni ynxu Fateema ta fi karfina, tunda yar nn ta taso take samu mgna, bata ji kwata kwata" inna da tuni ta hangame baki tana kallon Abba tace "uban me yake xuwa mata bayan saki ukun da ya dankara mata" Abba yace "wnn kuma ita xa ki tambaya baba, wae har ta bude baki da kanta tace min ae fa bae saketa ba, ki ce wnn yar ba mahaukaciya bace" inna ta juya tana kallon Ashnaah fuskarta a murtuke tace "to don uban ki me yake xuwa yi a anguwar nn, to wllh xan sa a tara sojoji bakin gate duk randa ya kuma xuwa su daure min shi har sae na xo, kun ji min gantalallen mutum" Ashnaah da tuni hawaye ya fara bin kuncinta bata ce komae ba kanta a kasa, inna tace "Aa'h kana da gskya Adamu dole kam a aurar da ita kar ma ya gudu min da jika in shiga uku" fashewa da kuka Ashnaah tayi ta mike da sauri ta nufi sama da kyar tana rusa kuka, Abba yace "kin gani ko, to ace baxan aurar da ita ba, nasan abinda suke kullawa da shi" Inna ta bi ta da kallo baki bude tace "anya tana da lfya ma kuwa yar nn, kuma dingishin me take hka" Abba yace "wae bugewa tayi" Inna tace "dama hka fateema ta xama ban sani ba" Abba yyi murmushi yace "bari ki ji ta ynda suka hadu da yaron har ya aureta" inna ta baxa kunnuwa tana sauraransa, Abba ya fayyace mata komae tun daga farko har kashe har ma da dalilin da yasa bae gaya mata gskya ba da farko, inna na huci tace "ae ko da xan ga wnn dan iskan yaron sae na shuka masa rashin mutunci wllh, maxa maxa a maido da auren sati biyu, ae Sadeeq jikana ne yaro dan arxiki, kakarsa kawata ce ssae. 88.... Karfe takwas da minti sha biyar na dare Najeeb ya shigo gidansu Khaleel, karasowa yyi cikin falon ya gaida dad din Khaleel dake xaune ya amsa masa snn ya Mike xae wuce sama, kiransa Dad ya kuma yi, Najeeb ya koma cikin falon tare da amsawa, dad yana kallonsa da kyau yace "sako dama xan baka ka kai ma abokin nake, tell him dat ni nace idan ya kuskura ya ja ma kansa wani ciwon wllh ya nemi wani uban bani ba don ko kallon inda yake ma ni baxan yi ba, iyaka ma ni kawae ya bar min gida kan wata yar matsiyata baxan tsaya tada hnklina a kansa ba idan ya ja ma kansa cuta" Najeeb yyi shiru bae ce komae ba Dad yace "you can go dats ol" juyawa Khaleel yyi ya nufi sama, kwance ya samesa kmr me bacci ga jerin coolers din abinci har uku a ajiye a dakin amma ko daya ba a taba ba, Najeeb na shigowa Ummi ma ta shigo dakin, tana kallon Najeeb tace "yauwa gwara da ka xo Najeeb, gskya Khaleel baxae sa min hawan jini ba a gidan nn, kan wani dalili yake neman cutar kansa a kan abinda shi ya ja, ka tambayeni yaushe rabon da ya ci abinci a gidan nn, ni fa bbu ruwana, da yasan yana sonta ya aureta don ya walakantata, ni dama tun farko ban yrda da auren nn nasa ba" Najeeb yace "kiyi hkuri xan masa mgna Ummi" juyawa tayi ta fice daga dakin, najeeb ya xauna gefensa yana kallonsa yace "meyasa baka cin abinci Khaleel" Khaleel ya mike xaune yace "baxan ci ba, y on earth baxa a tausaya min ba a gane ina cikin damuwa" Najeeb yace "to rashin cin abincin ne xae yaye maka damuwar" Khaleel ya dafe kansa da yyi masa nauyi a raunane yace "baxan iya rayuwa ba fateema ba, nobody seems to understand me, ta xame min jinin jikina" hawaye ne ya cika idonsa a Sanyaye yace "ban san xan fada tarkon so hka ba, na aurota ne don in wlknta ta, in ci mata mutunci...." Kasa ci gaba yyi ya runtse ido da kyar ya bude baki yace "nd yhu knw wat? I deeply fell in luv wit her lkci daya " Najeeb ya sauke ajiyar xuciya ya shafa kansa yace "I promise xan mayar maka da farin cikin ka, amma idan ka min alkawarin idan kun yi settle down kai da ita xa ku min hanyar auren twin sis dinta" Khaleel ya daga kai yana kallonsa, mikewa yyi yana masa mugun kallo yace "u re vry selfish, sae ma idan xa muyi maka hanya xaka taimaka mana ko? Toh hold on to ur help malam" juyawa Khaleel yyi ya shige bathroom, Najeeb yyi murmushi yana shafa kansa a xuciyarsa yace "ba taimakon kke so ba knn" Ashnaah na kwance can cikin dare bacci ya gagareta duk abin duniya ya isheta, kukan ma ynxu ta neme shi ta rasa, wani xafi xuciyarta ke mata ba kadan ba, sae juye juye take tana kiran Allah a xuciyarta, wayar Khaleel dake gefenta yyi haske ta Mike xaune da sauri ta dauka don dama kiransa kawae take jira, tana dagawa ta sakar masa kuka, duk ya rikice yana tambayarta me ya faru kuma, ita kanta bata san dalilin kukanta ba, da kyar ta iya cewa "I just can't do without yhu, I love yhu" a sanyaye Khaleel yace "I love yhu 2 swthrt" ji yyi kmr tana kusa da shi ya rungume abarsa ko xae ji sanyin xugin da xuciyarsa ke masa, a hnkli yace "ki kwanta ki huta kin ji wife, promise me baxa ki sake kukan nn ba" gyada masa kai tayi kmr yana ganinta, ya lumshe ido yace "to kiyi addu'a ki kwanta kin ji" ta kuma gyada masa kai, a hnkli yace "I love yhu dear" a sanyaye tace "I luv yhu more" Khaleel yyi murmushi yace sweet dreams, snn ya katse kiran, Ashnaah ta koma ta kwanta a hnkli ta lumshe idonta nn da nn bacci ya dauketa. Hka kwanaki suka dinga ja Ashnaah da Khaleel suka kasa neman ma Kansu mafita, Bbu abinda ke daga ma Ashnaah hnkli irin ynda taga ana ta shirye shiryen bikinta da Sadeeq, ko nn da falonsu Abba ya hanata saukowa kullum tana daki kmr mayya tana aikin kuka, cikin dare ne kadae take samun waya da Khaleel sbda Ashfah da wata cousin sis dinta dake gidan sun sa mata ido, ana saura kwana biyar bikinta da Sadeeq aka kawo sadaki da kayan lefe da safe, ranan an ga tashin hnkli gun Ashnaah don ihu ta dinga masu tana rusa kuka a gidan tana cewa ita mijinta bae saketa ba, sae da momy ta wawwanke ta da mari suka samu lfya a gidan, da yamma tana xaune kasan daki ta hade kanta da gwiwa, su Ashfah da cousin sis dinta Rahmah na xaune da kanwar momy suna ta hira bbu wnda ya bi ta kanta, don tun safe take a hkn, Autarsu momy ce ta shigo dakin rike da plate din farfesun kayan ciki da momy tayi ma Ashnaah tace a kai mata, don mugun tausayinta yar tata take kawae tana shassharewa ne sbda mai gidanta. 89..... Salma ta duka gaban Ashnaah tana kallonta tace "Ashnaah momy tace a kawo maki" Ashnaah ta dago kanta tana kallon smll mum din tata da idonta da ya kumbura, ajiye kulan Salma tayi gabanta ta bude mata tace "ki daure ki ci don Allah kin ga ko breakfast kin ki yi" Ashnaah ta kauda kanta da sauri da kamshin farfesun ya bugeta, ji tayi cikinta ya hautsine nn da nn amae ya xo mata ta mike da sauri ta nufi bathroom da gudu kan ta karasa ciki ta shiga kwararo amai, mikewa salma tayi da sauri ta nufeta, hka ma sauran mutanen da ke dakin, amai kawae Ashnaah take kmr xata amaye hanjin cikinta gashi bbu abinda ta ci tun jiya, durkusawa Ashfah tayi kusa da ita ta dafata tana mata sannu, Salma ta shiga bayin ta debo Mata ruwa ta wanke bakinta snn ta mike jiki ba kwari ta nufi gado ta kwanta suka gyara gun aman, nn da nn bacci ya dauke Ashnaah, momy suka kira ta shigo dakin tana kallon yar tata ta taba jikinta ta ji xafi, hkn yasa ta fita ta je ta samu Abba tace masa Ashnaah bata da lfya, ba tare da ya kalleta ba yace "a siya paracetamol a bata" wayarsa dake ring ya daga ya mike ya fice daga falon yana amsa wayar, hawaye ya cika idon momy don ko kadan bata son abinda yake ma Ashnaah, a sanyaye ta mike ta nufi dakinta ta dauko kudi ta ba su Ashfah driver ya kai au pharmacy su hado Mata maganin xaxxabi tukun. Washegari Ashnaah na kwance sae juye juye take ta rasa inda xata sa kanta don wani mugun xaxxabi ne jikinta duk da magungunan da take sha, ga wani tashi da xuciyarta ke yawan yi, ko wani irin abinci ta gani nn da nn amae xae xo mata, Ashfah ce ta shigo dakin tana kallonta tace "Sadeeq na jiranta a waje" bbu musu ta mike da kyar don wani jiri ne je kwasarta, ta sa hijab snn ta fita, yana xaune kan farin kujerar roba a compound din yana jiranta, kujera ta ja ta xauna da sauri ganin faduwa take shirin yi, yana kallonta yake "wae ba ki jin ddi" kae kawae ta gyada masa yace "to ko mu je asibiti ne" ta girgixa masa kai da kyar tace "ina shan magani" ko mgna bata son yi sbda ita kadae tasan abinda take ji, ta dago tana kallonsa murya can kasa tace "don Allah gidan wata kawata nake son xuwa, nasan Abba baxae bar ni ba, ka taimaka min kayi masa mgna sae kace kai xaka kai ni" yace "OK yana ciki ne" gyada masa kai yyi ya mike ya nufi cikin gidan, ko kadan ita kam Sadeeq baya bata haushi, tana nn xaune ya fito daga gidan yana kallonta yace "ki shirya ki tafi nayi masa mgna, idan kuma kina son in kai ki ne toh" ta girgixa masa kai tace "aa xan je ni kadae, ka jira in shirya amma sae mu fita tare" yana nn tsaye yana jiranta ta fito bayan ta gama shiryawa snn suka fita a tare ya bata kudin mota ya kama gabansa, a dai daita sahu kawae ta hau ba tare da tasan inda xata ba, ta shiga kiran khaleel, yana dagawa ta gaya masa su hadu a sch kawae don can ne kadae take tunanin asirinta baxae tonu ba, kusan a tare suka shigo makarantar, Khaleel yyi mugun farin cikin ganinta ya rungume abarsa cikin mota ta shiga rera masa kuka a hnkli, dago kanta yyi a sanyaye yace "baki da lfya ne, ur temperature is high, wats..." shiru yyi ya kasa ci gaba yana kallonta, ta sunkuyar da kanta tana share hawayen fuskarta tace "ina shan magani ae" kamo hannunta Khaleel yyi yana kallon fingers dinta a sanyaye, ta kwanta jikinsa tana hawaye tace "ni baxan iya rabuwa da kai ba." ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 90.... A hnkli Khaleel ya dago kanta yana kuma kare ma fuskarta kallo kmr ne son gano abu, ita ma ta daga manyan idanuwanta tana kallonsa, saketa yyi lkci daya da sauri yace "wani maganin ki ke sha a gida?" Murya can kasa tace "na xaxxabi aka siya min" bude motar taga yyi ya koma driver seat da sauri ya tada motar, a dan tsorace tace "ina xa ka kaini kuma, don Allah ka bari in tafi gida kadda Abbana ya fara nemana, ya juya yana kallon da damuwa yace "magunguna xan siyo maki wife ba wani gu xan kai ki ba" shiru tayi tana kallonsa, yyi reverse suka kama hanyar fita daga makarantar, gidansa ta ga ya nufa da ita, ta hade rae tace "don Allah ka ajiye ni in koma gida doctor," parkin yyi ya juya a dan sanyaye yana kallonta yace "baki son in duba ki ne wife" bata ce komae ba amma ta daure fuska, driving dinsa ya ci gaba a sanyaye, ya nufi wani pharmacy ya siyo mata magungunan da yasan ya kamace ta, duk ya fiffido su daga kwalinsu ya xubar a shara don kar ta ga ko na menene snn ya nufi cikin motar, tana xaune ta jinginar da kanta jikin kujera, ita kanta tasan daurewa kawae take duk da ta rasa me ke mata ciwo, bayan ya shiga cikin motar yace "kin ci abinci?" Gyada masa kai tayi duk da bata ci ba don bbu abinda taji ke ranta, nuna mata ynda xata sha magungunan yyi snn yace "kar ki kuma shan ko wani maganin xa a baki, kin ji ko wife" gyada masa kai tayi nn ma snn ya nufi gida da ita, nesa da gidansu ta sa ya ajiyeta Snn ta karbi ledan maganin hannunsa ya kamo hannunta yana kallonta yace "ki ajiye wayar ki kusa da ke plss xan kira ki" kai ta gyada masa snn ta fice daga motar da sauri, ya bi ta da kallo har ta shige gida, ajiyar xuciya ya sauke lkci daya murmushi ya bayyana a fuskarsa. Bata samu kowa falo ba hkn yasa ta nufi sama da sauri ledan maganin hannunta na cikin hijab dinta, kan gado ta nufa ba tare da ta kalli su Ashfah da ke xaune dakin ba ta kwanta tana mayar da numfashi kmr warce tayi gudu, Salma tace "har kin dawo?" Ashnaah ta gyada masu kai kawae ta juya don bata son mgna. Har ta fara bacci Ashfah ta tasheta wae Abba na kiranta, da kyar ta iya mikewa xaune ta dauki hijab dinta ta sa snn ta mike ta fita daga dakin, Abba na xaune falo ta karasa a dan sanyaye gabanta na faduwa don bata san me xae ce Mata ba ta durkusa ta gaishesa, ya amsa ba tare da ya kalleta ba shiru tayi tana jiran jin me xae ce, soye soye momy ke yi a kitchen hkn yasa xuciyarta ya shiga tashi ssae, duk ta rikice jin hautsinewar da cikinta yyi, sae jira take Abba ya sallameta ta bar falon, amma Abba na ta danna laptop, bata ankara ba lkci daya aman ya xo mata ta toshe baki ta mike da gudu da nufin komawa sama tayi aman, amma tana kaiwa dai dai stairs ta shiga kwararo aman, mikewa Abba yyi yana kallonta, momy ma ta fito da sauri jin kakarin amai, tana ganin Ashnaah ce ta nufi stairs din da sauri tana tambayarta me ya sameta, kasa bada amsa tayi amai ya ci karfinta, ganin ynda take aman kmr xata amayo hanjin cikinta yasa Abba ya karasa wajen shi ma, momy ta dagota tana mata sannu da damuwa, wani aman ya kuma xuwa mata ta dingi yi ba kakkauta, hnklin momy ya tashi ssae, Abba ya ciro wayarsa ya shiga neman layin likitansa, sae da Abba ya gama waya da likitan snn yana kallonta yace sannu, kai kawae ta gyada masa don ko amsawa bata iya aman yasa tayi weak ssae, ya juya yana kallon momy yace "ki tafi da ita daki ynxu likita xae xo" da taimakon momy Ashnaah ta gyara jikinta a bathroom snn ta dawo cikin dakin ta kwanta nn da nn bacci ya dauketa. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 91..... Cikin minti talatin da yan mintuna likita ya iso gidan, har lkcn Ashnaah na bacci a daki, Ashfah ta shigo dakin ta xauna gefenta ta shiga tada ta, mikewa xaune Ashnaah tayi da kyar, Ashfah ta mika mata hijab dinta tace "ga likita ya xo, Abba yace ki sakko kasa in xa ki iya" Ashnaah ta girgixa mata kai kawae don bata son mgna, Ashfah tace "to ki sa hijab bari likitan ya shigo" da taimakon Ashfah Ashnaah ta sa hijab dinta snn Ashfah ta fita don cewa likitan ya shigo, da sallama likitan ya shigo dakin Abba na biye da shi a baya, Ashnaah ta sakko da kafafuwanta kasa daga kan gadon, likitan da baxae wuce shekaru 38 ba ya karaso yana kallonta yace "sannu," sunkuyar da kanta tayi, likitan yyi shiru yana kallonta, hkn yasa ta daga kai ta kallesa, Abba dae na tsaye Kansu, "ina ke maki ciwo?" Tambayar da likitan yyi mata knn, da kyar ta iya bude baki tace "ni ma bn sani ba" likitan ya juya yana kallon, Abba yace "in baku waje ne?" Murmushi likitan yyi tare da gyada masa kai, Abba yace "OK" snn ya juya ya fita, da mugun mmki likitan ke kallonta yace "Amma an mayar da auren ku da mai gidan ki koh? I mean kuna tare da mijin ki ynxu?" Girgixa masa kai Ashnaah tayi, ya dan xaro ido yana kallonta xae yi mgna sae kuma ya fasa ya shiga fiddo da kayan aikinsa a dan 1st aid box din da ya xo da don yana son tabbatar da abinda ya gani tukun, ita dae Ashnaah sae kallonsa take, cikin mintuna da ba su wuce sha biyar ba yyi duk abinda ya kamata snn yace mata xae je lab ya dawo, falo ya samu Abba yana cin fruit salad, ya karaso cikin falon yace "Alhaji bari in je inyi test na dawo ynxu, na dibi jininta ne" Abba yace "to amma kadda ka dau lkci Dr, I want her to get well soon don in 2dayz tym she will be wedded" likitan yace "in sha Allah" Bayan minti talatin likitan ya dawo gidan, A balcony ya samu Abba yana waya, Abba ya katse wayar yana kallon likitan yace "me sakamakon ya bada" likitan da duk ya daburce yace "bari dae ina xuwa Alhaji" cikin gidan ya nufa ya haura sama, da sallamarsa ya shiga dakin ya sameta ta dukunkune cikin bargo ta rufe har kanta, su Ashfah da Salma duk suna dakin suna gwada ankon da aka fidda na bikin Ashnaah da xa ayi jibi an karbo masu daga gun tela, Ashnaah na jin an shigo dakin ta bude kanta a hnkli, ganin likita ne yasa ta Mike xaune, kallon su Ashfah ya tsaya yi sae kuma yace "xa ku dan ba mu waje yan Mata" duk suka fita daga dakin, ya karaso ciki yana kallon Ashnaah ya ja stool din gaban madubi ya xauna har lkcin bae daina kallonta ba yace "Me yasa kika xabi lalata rayuwarki ki ba iyayenki kunya Fateema" Ashnaah ta daga Kai da mmkin jin furucinsa tana kallonsa, ya girgixa kai yace "kin ce min ba a mayar da auren ku ba, na kuma ji dad din ki na cewa jibi ne auren ki, sae ga shi sakamakon gwajin da nayi maki ya nuna kina dauke da cikin sati biyu da kwana shidda, hw is dat?" Ashnaah da komae nata ya tsaya ta gwalalo ido a mugun tsorace tana kallonsa, lkci daya abinda ya faru tsakaninta da Khaleel ya fado mata, a rude tace "Ni doctor" ya ajiye mata result din test din gabanta yace "yes! Check for ur self" Ashnaah ta daura hannu a ka cikin tashin hnkli tace "wayyoo Nashiga uku na lalace ciki kuma Doctor" wani matsanancin kuka ta fashe da ta sakko da sauri don kawae ji tayi karfi ya xo mata ta durkushe gabansa cikin kuka tace "don Allah don Annabi don darajan iyayen ka kayi min rai ka rufa min asiri doctor ka taimaka min" kuka ssae take a gigice, likitan ya girgixa kai yace "taya xan taimaka maki a nn fateema, ynxu dae who is responsible" Ashnaah ta kuma fashewa da wani sabon kuka ta ma rasa me xata ce masa shknn Khaleel ya cuceta ya kai ta ya baro ta, ita kam tasan bata da sa'a a rayuwa, likitan dae sae kallonta yake yana jiran amsa, cikin kuka tace "doctor mijina ne wllh, ni bn taba iskanci da kowa ba" likitan yace "wani mijin kuma, kin kuma aure ne" rasa abun cewa Ashnaah tayi sae kuka take ssae, shi dae sae kallonta yake, can dae ta gaji ta tsaida kukan tace "doctor ka tausaya ma rayuwata ka cire min cikin nn kashe ni wllh Abba xae yi, help me plss" likitan ya mike yana girgixa kai yace "of course bna hka, ynxu dole in kai ma dad din ki result din don abinda yake jira knn, I was called to check on wats wrong with yhu, xuwa xan yi ince bbu komae?" Ashnaah ta fashe da kuka ta tsaya gabansa a rikice tace "wayyo doctor help me plss kasheni xae yi kace masa malaria ne plss" likitan ya dan yi murmushi yace "its nt possible, a bakin aiki na fa nake kuma kudi xae biya ni sae in masa karya, to wae ma wa yyi maki cikin nn ki gaya min?" Cikin kuka Ashnaah tace "nace maka mijina ne wllh bae sakeni ba, set up aka yi masa, but no one is willin to blive dat" likitan yyi shiru duk da ba yrda yyi ba yace "meyasa xa ki amince masa batun kin san da hka," Ashnaah ta durkushe kasa tana rusa kuka tace "he forced me wllh" Likitan ya sauke ajiyar xuciya snn yace "amma kinsan dole in kai result din nn dae ko" shiru Ashnaah tayi tana hawaye, likitan yace "shknn let me c if I can cool ur dad down nd explain thingz to him, don dole in kai masa sakamako ya gani" kasa cewa komae Ashnaah tayi, duk jikinta yyi sanyi ta ji kmr Yau ce ranan mutuwarta, likitan yace "ki kwantar da hnklin ki xan yi kkrin ganin na nuna masa mijin naki bae sake ki ba as u said" yana kai wa nn ya juya ya fice daga dakin, Ashnaah ta Mike da kyar tana hawaye ta shiga tunanin abun yi hnklinta a tashe don tasan ko ruwan sanyi xae xama baxae taba convincing Abba ba, Likitan na shiga falon Abba ya samesa yana kallon news, momy kuma na xuba masa abinci kan centre table, Abba na kallon likitan yace "me sakamakon ya nuna doctor, har ka gama treatin din nata ne" likitan ya sauke ajiyar xuciya yace "Sorry to say Alhaji sakamako ya nuna yar ka na dauke da juna biyu na sati biyu da kwana shidda" mikewa Abba yyi tsaye da sauri ya saki remote din hannunsa ya xare glass din idonsa da karfi yace "wat?" Momy kam sake ruwan glass din hannunta tayi ba tare da ta sani ba, likitan na gyada kai yace "hka sakamakon gwajin da nayi Mata ya nuna Alhaji In'sha Allah" ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 92..... Juyawa Abba yyi yana ma momy wani irin kallo har lkcn mmki bayyane a fuskarsa, kuka momy ta saki tana kallon likitan tace "ciki fa kace doctor" likitan ya mika masu takardan hannunsa snn ya kara da cewa "amma ta nuna min auransu da mijinta na nn, don hka kar kuyi saurin yanke hukunci, bincike shine abinda..." Wani kallo kawae Abba ke masa, bae Bari ya Kai aya ba yace "ka gama aikin ka yallabae, xan turo driver da kudin ka anjima, tnx 4 ur help" Ashnaah kam tun bayan fitan likitan take ta rusa kukan tashin hnkli ta rasa abun yi, tasan yau kila sae dae wata ba ita ba, duk sae ta nemi xaxxabi da kasalan da take ji ta rasa, mikewa tayi xuciyarta na bugawa ta dauki hijab din ta tasa snn ta dauki wayarta ta fice daga dakin, su Ashfah da shigowarsu knn suka shiga tambayarta lfya amma ko ta Kansu bata bi ba, sakkowa kasa tayi ba tare da ta kalli kowa na falon ba ta nufi kitchen da sauri, dai dai lkcn da Abba ke sallaman likitan sa knn fuskarsa a daure jin maganganun da yake kkrin kawo masa, juyawa Abba yyi ganinta ya daka mata wani mugun tsawa yace "ina xa ki," Ashnaah bata ko kalle inda yake ba ta shige kitchen a guje ta bude kofar da xae sada ta da garden ta fice, Abba na ganin hka ya bi ta gaban gidan da sauri shi ma, likitan ya bi bayan sa, momy kam xubewa kan kujera tayi tana kuka ssae su Ashfah suka sauko suna tambayarta lfya amma ba bakin mgna, tunda Ashnaah take bata taba irin gudun da tayi ba ranan don kan kace kwabo har ta isa gate, dai dai sanda Abba ya fito knn cikin tsawa yake ce ma mai gadinsa ya rufe masa gate kar ya bari ta fita, kuka Ashnaah ta saki ganin mai gadin ya kulle gate din ga Abba na tahowa, ta durkushe gabansa tana rusa kuka hnklinta a tashe tana cewa "don Allah don annabi kayi min rae ka bude min, kashe ni xae yi wllh" Tahowa kawae Abba yake fuskar nn tasa bbu alamar rahama idon nn nasa ya kada, hkn ya kuma tada hnklin Ashnaah ta shiga kwala ihu, tun kan Abba ya karaso mai gadin ya shiga basa hkuri duk da bae san me ke faruwa ba, amma ko kadan Abba bae Ma san yana yi ba, likitan ya sha gabansa da sauri yace "Haba Alhaji kar ka ce xaka taba ta don Allah, consider situation din da take ciki kar ka ji ma yar ka ciwo, ka kwantar da hnklinka ka saurari bayanin ta tukun" Abba ya tura likitan daga gabansa cikin tsawa yace "gwara in kasheta kawae yau in huta" Ashnaah na jin hka ta shiga gudu tana xaga gidan tana rokon Abbanta cikin kuka, tana ganin momynta ta fito ta nufeta da gudu ta tsaya bayanta tana cewa ta taimaka mata don Allah, Ashfah da tuni ita ma ta fara kuka ta nufi Abbansu ta durkushe gabansa cikin kuka take cewa "don Allah don Annabi Abbanmu kayi hkuri" cikin kuka momy tace "wllh Adam kar ka kuskura ka taba min 'ya ta da ka taba ta gwara ka Kore mu gaba daya gidan yau" Abba ya tsaya kallonta can yace "hka kika ce koh" kai tsaye momy tace "ehh hka na ce" Abba yace "fine, Ni baxan ma Fateema baki ba amma daga yau na cire ta cikin 'ya ya na, wato na yafe ta, kar ta kara tunanin tana da uba a duniya, ba ita ba gidan nn, snn idan ta kuskura ta sa kafa ta taka gidan mahaifiyata bn yafe mata ba, ta tafi duk inda xa ta bnda gidan uwata, bn haifi yar da xata ja min abun kunya a duniya ba" cikin tsawa Abba yace "ta xo ta fice min a gida" Momy tace "in har Fateema ta bar gidan nn to ni ma na bar gidan nn" Abba ya daga kafada yace "fine! Ki tafi amma a bakin auren ki" Abba na kai wa nn ya nufi cikin gida da sauri, Ashnaah ta kuma fashewa da wani matsanancin kuka tana kallon momynta tace "A'a momy kiyi hkuri, Kar ki ce hka, amma ki yafe ni don Allah nasan tun tasowa ta na kasance warce bata jin maganarku amma momy ni ban taba bin maxa ba duk rashin ji na, ki yrda dani momy mijina bae sakeni, tun daga ranar da na ga takardan nn nasan bashi ne ya rubuta ba don ba ma shi da lfya ranan da na ga takardan, snn ya sha gaya min baxae taba saki na ba idan na bukaci hkn tun farkon aurenmu lkcn ma ba ddin xaman gidan nake ba, amma da yake na dde ina son ya sakeni shi yasa na dauka takardan kawae na dawo gida duk da raina bae so hkn ba, nasan ko min daren ddewa gskya xata bayyana kuma Abbana xae yafe min." Ashnaah tayi shiru tana kallon momynta da ke hawaye har lkcn, can ta juya ita ma tana hawayen tace "ki daina kuka momy xa mu dinga waya, amma ki taimaka min ki ba Abbana hkuri" Ashnaah na kai wa nn ta soma tafiya ta nufi gate, Ashfah ta bi ta da sauri tana kuka tace "ina xa ki sister" Ashnaah ta share hawayenta tace "gidan mijina xan koma" tana fadin hka ta bar gun da sauri ta bude gate ta fice daga gidan. Plss sisters ku bar ni in rubuta littafina ynda na tsara, wnda ya ga littafin nn yyi masa ya karanta wnda kuma ya ga bae masa ba ya bar shi kawae, nt dat xa ayi ta min complain ace hka ya kamata in yi ba hka ya kamata in yi ba, hkn bbu ddi Sam, hka aka min lkcn littafin Ikram, gskya ni dae bna jin ddin hka. 5 mins · Khaleesat Haiydar... ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 93..... Tafiya kawae Ashnaah take ba tare da tasan inda xa ta ba gashi bata fito da kudi ba bare ta sami abun hawa ta hau, gajiya tayi ta nemi dakalin wani da shago ta xauna ta dalilin jirin da take ji ssae ga kasala, lkci daya taji xaxxabin ya dawo mata, wayar da ke hannunta ta kalla don ta ma manta ta taho da shi, nn da nn ta shiga neman layin Khaleel taji bbu kudi a wayar, dafe kanta tayi ta rasa me ke mata ddi ga wani aman da ke taso mata, gun kwanciya kawae take nema a lkcn, pls cal me ta tura masa da sauri bayan kusan minti goma ta ga bae kira ba, ta kuma tura masa ta jira still bae kira ba, ta kusa minti talatin a xaune kanta hade da gwiwanta can dae ta dago a hnkli tana tunanin abun yi, tasan ko taku daya baxa ta iya ba daga wajen faduwa kawae xata yi tsabar jirin da take ji, wasu hawaye ne su ka shiga bin kuncinta ita kam ko me yasa bata da sa'a a rayuwa, a hnkli ta shiga bin inda take da kallo tana tunanin to ko taimako xata nema don gun Akwae mutane da dama suna ta harkan gabansu, ji tayi baxata iya tashi ba kawae ta ci gaba da xamanta a gun, Sadeeq ne ya fado mata, ta dago wayar a hnkli tana kallon screen din, please cal me ta tura masa shi ma, Sadeeq dake xaune kasa falon Abba da dad dinsa ya ciro wayarsa jin alert din msge, ganin sakon yasa ya mike ya ce yana xuwa snn ya fita, kiranta yyi bugu daya Ashnaah ta daga da sauri, Sadeeq yace "ya aka yi Fateema," a sanyaye Ashnaah tace "kati xaka turo min don Allah" Sadeeq yace "me yasa kika yi abinda kika yi?" Ashnaah da hawaye ya shiga bin kuncinta tace "sbda mijina bae sake ni ba" Sadeeq ya dan yi shiru snn yace "kina ina ynxu?" A hnkli tace "gidan mijina xan je, ina son kiransa ne bni da card" Sadeeq yace "Shknn, Allah ya huci xuciyar Abban ki ya sassauta maki" kai kawae Ashnaah ta gyada masa kmr yana ganinta tana hawaye, yace "xan maki transfer ynxu" yana kai wa nn ya katse kiran, cikin minti biyu taga transfer din dari biyar ta tura masa da text din gdya, tana kkrin dailin nmbr Khaleel kiransa ya shigo, dagawa tayi bata ce komae ba, da damuwa yace "wife kiyi hkuri sae ynxu na ga text din ki, am srry I wasn't OK ne xuciyata na damuna shine nayi alluran bacci, I just woke up ynxu" kuka Ashnaah ta sakar masa, nn da nn ya rikice mata yana tambayarta me ya faru ta kasa cewa komae sae kuka, ganin ynda ya birkice ya sa a sanyaye tace "Ka kuma hada ni da parent dina hnklin ka ya kwanta, ba ka min adalci ba, sae in iya cewa ka cuce ni ma kawae, me yasa ka min hka doctor...." Kuka ne ya ci karfinta ssae, Khaleel da hnklinsa yyi mugun tashi duk da ya gano dalilin maganganun nata yace "plss ki gaya min me ya faru, kina ina ne?" Cikin kuka ssae tace "ba dole ka tambaye ni ina ina ba" kmr xae mata kuka yace "plss wife kar ki bari a cire cikin nn am beggin yhu ki tausaya min don't let dat plss, ki bari mu ga bbynmu" Ashnaah da mmki ya cika ta ta ma rasa me xa ta ce masa, wato ashe ya ma san tana da ciki knn, Shiru tayi tana naxarin magungunan da ya bata ranan har yana cewa kar ta kuma shan ko wani magani xa a bata a gida, kuka ta fashe da tace "wllh baka da imani, ka hada ni da iyayena kawae ka raba ni da su don son xuciyar ka, to bana son cikin xubar wa xanyi" kuka kawae take kmr ranta xae fita ta katse kiran, Khaleel da idanunsa suka kada suka yi ja ya dafe kansa da ke Sara masa xuciyarsa nai masa kuna. Kiranta ya kuma yi, Ashnaah da ke kuka har lkcin ta kasa kin daga kiran nasa duk da ta so yin hkn, ta dauka tayi shiru, a sanyaye yace "kiyi hkuri fateema xan cire maki cikin na maki alkawari tunda ba kya so, ynxu plss ki gaya min inda ki ke" taki cewa komae na wani dan lkci snn a hnkli ta gaya masa inda take, cikin mintunan da ba su wuce sha takwas ba Khaleel ya iso gun da ta gaya masa take, yana gama parkin ya fito ya nufi inda ya hangota da sauri ya durkusa gabanta ya kamo hannunta da damuwa yace "am vry srry wife, I caused all dis" kuka ta sakar masa, duk ya rikice yana lallashinta, ganin taki yin shiru yasa dago ta ya rungume abarsa, ta tsaida kukan da take da sauri ta kwace kanta ganin a titi suke, kama hannunta yyi tana ganin jiri har suka isa motarsa snn ya bude mata front seat ta shiga, ya xaga ya shiga shi ma ya tada motar suka bar wajen, ssae ta ba Khaleel tausayi ganin ynda ta da da ramewa da ganinta ka ga mai laulayi, ga kuma kukan da ta ci, kwantar mata da kujerar motar yyi ta kwanta, nn da nn bacci ya dauketa, gidansa ya nufa da ita, yana gama parkin ya fito ya dauki abarsa ya shiga ciki da ita, ta bude ido da sauri tace "meye hka" bedroom dinsa ya shiga da ita, ya cire bedsheet din kan gadon snn ya kwantar da ita. 94..... Mikewa xaune tayi da sauri ta wani daure fuska don haushinsa kawae take ji, a sanyaye yace "srry na ga kina bacci ne" ta dauke kanta kawae har lkcn fuskarta a daure, mikewa yyi jiki ba kwari ya fita daga dakin ta bi sa da kallo, hawaye ne ya shiga bin kuncinta duk she is confuse fushinta xata nuna masa ko jawo mijinta xata yi jiki. Jinginar da kanta tayi jikin gadon tana tunanin rayuwarta tun daga ranan da ta fara haduwa da Khaleel, wasu hawaye masu xafi suka shiga sakko mata, tana nn a hka har bayan minti talatin ta ji an kira sllhn Azahar, mikewa tayi a hnkli don xuwa tayi alwala taji jiri ya debeta ta dafa bango da sauri kan ta kai kasa ta koma kan gadon ta xauna, kasa mikewa tayi har aka idar da sllh Khaleel ya shigo dakin, ba karamin tausayi ya bata ba yanayin da ya shigo, ya karaso gabanta ya duka ya ajiye mata ledan abincin hannunsa da plate yace "ga abinci na siyo maki ki sakko ki ci" kallonsa kawae take ya bude abincin ta ga dafa duka ne da naman kaxa, nn da nn cikinta ya hautsine aroma din abincin na bugar ta, mikewa ta shiga kkrin yi da sauri ya lura da hkn ya mike yace "me ya faru, amae kike ji" toshe bakinta tayi ta sakko daga kan gadon tayi baya xata fadi ya kamota da sauri ta durkushe kasan dakin ya bi ta har lkcn yana rike da ita ta shiga kwarara masa aman a jiki, ssae ta bashi tausayi ganin bbu komae cikinta, gashi she is too young ace tana da ciki ynxu, yana rike da ita yana mata sannu a sanyaye har ta gama ta fada jikinsa tana mayar da numfashi ya rungumeta, sun fi minti biyar a hka snn ya dago kanta a hnkli yana kallon idonta da yyi ja yace "Sannu wife" sunkuyar da kanta tayi kawae, mikewa yyi ya dauketa suka nufi bathroom, da kansa ya gyara mata jikinta bayan ya cire mata kaya, snn shima ya gyara nasa jikin ya daukota suka fito ya kwantar da ita kan gado ya lulluba ta da bargo snn ya shiga gyara dakin, ko da ya gama har tayi bacci ya xauna gefen gadon a hnkli yana kallon kyakkyawan fuskarta wani mugun shaukin sonta na fixgarsa, yasan he can't do without Fateema, daura hannunsa yyi a hnkli kan goshinta ya ji xafi ssae, ya mike ya fita xuwa kitchen ya hado Milo kawae ba madara ya dawo dakin snn ya shiga tashinta a hnkli, bude ido tayi tana kallonsa, ya dago ta yace "ki daure ki sha tea plss sae in ba ki magani, jikin ki yyi xafi" girgixa masa kai tayi da kyar tace "Amae xan yi" rungume ta yyi yace "A'a baxa ki yi ba ruwan tea ne kawae, ki rufe idon ki ki shanye ynxun nn" girgixa masa kai tayi alamar baxa ta sha ba don ta kasa mgnr ma gaba daya, ya dauko tean ya dago kanta, ta sakar masa kuka tana girgixa kai, da kyar ya lallabata tayi sip uku don bbu xafi, yyi yyi da ita amma ta ki karawa, rungumeta yyi ya shiga shafa bayanta a hnkli ganin amae take son yi, har sae da ya ga ya fada mata snn ya kwantar da ita yace yana xuwa, makullin motarsa ya dauka ya fita ya nufi pharmacy ya siyo magunguna da allurori ya dawo ya sameta tana bacci, yana cikin hada alluran wayarsa da ya ajiye gefen gadon yyi ring, ya dauko wayar yana kallon screen din ya ga Dad dinsa ne me kiran, gabansa ya fadi don har ya manta rabon da ya kirasa, 'karan wayar ya tada Ashnaah ta shiga juye juye don wani ciwo da taji cikinta ne ko mararta ne ta kasa tantance wanne ne ke mata ciwon, mikewa Khaleel yyi ya daga kiran, gabansa na ci gaba da faduwa yyi sallama a hnkli, "Maxa maxa ka xo ynxun nn ka same ni a gida duk inda kke" abinda ya ji dad dinsa ya ce knn ya katse kiran a take, Khaleel ya ajiye wayar a sanyaye ya juya yana kallon Ashnaah ya karasa kusa da ita da sauri ya dagota yace "me ya faru" ta fashe da kuka tace "wayyo Allahna ciwo yake min" da damuwa yace "ina?" Taki cewa komae sae kuka take tana yarfe hannu, allurorin da ya gama hadawa ya dauko don yi mata, da kyar ya samu yyi mata don ta basa wahala ssae, ya rungumeta yana lallashinta ta gaji da kukan tayi shiru don kanta daga karshe bacci ya dauketa. 18 mins · Khaleesat Haiydar... Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 95..... Mikewa Khaleel yyi bayan ya lullube ta ya koma can gefen gado ya xauna ya dafe kansa yana tunanin kiran da Dad dinsa yyi masa na gaggawa, juyawa yyi yana kallon Ashnaah, can ya Mike yana kallon agogo ya ga uku da rabi ya dauki car key dinsa ya fice daga dakin don xuwa amsa kiran dad din nasa don ya san baxata tashi ba a lkcn, ana kiran sllhn La'asar ya isa gidan, sae da ya fara shiga masallaci yyi sllhn snn ya shiga gida, Ummi na kitchen da rukayya suna girki, ya shiga kitchen din ya gaida umminsa, ta amsa masa ba tare da ta kallesa ba, jikinsa yyi sanyi jin irin amsawar da Ummi tayi masa, yana kallon rukayya yace "Abba fa?" Rukayya tace "yana falonsa" a sanyaye Khaleel ya nufi falon dad dinsa a Sama yyi sallama ya shiga, xaune ya sami dad din nasa da amininsa sae kawunsa, ya nemi kasa daga gefen kawunsa ya xauna ya gaishe su kansa a kasa, Kawunsa kadae ne ya amsa, Dad dinsa ya mike yana masa mugun kallo yace "me na gaya maka kwanaki Khaleel" shiru Khaleel yyi bae ce komae ba, ya daka masa tsawa yace "are yhu daft?" Khaleel ya dago a hnkli yana kallonsa still bae ce komae ba, Dad yyi murmushin takaici yace "har ni xaka dinga ja ma ana biyo wa har gida ana ci ma mutunci ko Khaleel," sunkuyar da kai Khaleel yyi kawae, Kawunsa yace "wae yarinyar nn ita kadae ce mace a duniya Ibrahim, yau ko da ace baka saketa ba baxa ka iya rabuwa da ita ba ko dan tijaran da mahaifanta ke ma ubanka?" Dad yace "to bari ka ji khaleel wllh daga yau ka kara nuna kasan yarinyar nn ba ni ba kai har abada, maxa maxa ka sallameta ta koma inda ta fito idan ba hka ba ka ga bacin raina, na haneka da kara interact da ita bbu kai ba ita, na raba ka da yar matsiyatan nn daga yau ta je can ta karata, kuma duk inda xa mu shiga ka amsa cikin da ke jikinta na ka ne bn yafe maka ba, tashi ka ban waje malam" Khaleel da tun fara mgnr Dad dinsa xufa ke karyo masa ya dago kai da kyar yana kallon dad din nasa da idanuwansa da suka kada, Alhaji mukhtar ya daka masa tsawa yace "uban me kke jira mister man, c'mon get lost" hawaye ne suka shiga sakko masa da kyar yana girgixa kai yace "Dad ni bn saketa ba wllh matata ce har ynxu, kayi hkuri dad I can't deny her pregnancy" bae rufe baki ba dad ya sauke masa mari, tunda yake a iya saninsa Dad dinsa bae taba marin sa ba sae ranan, Khaleel ya kasa dago kansa cikin tsawa dad yace "har ni xaka bude baki kana gaya ma wnn mgnr? to wllh Khaleel I mean my wordz idan har baka rabu da yar marasu mutuncin nn ba bbu ni bbu kai, shari'a fa ubanta yace xae yi da mu," Khaleel ya dafe kansa har lkcn yana hawaye yace "kayi hkuri Dad idan nace xan guje ta ban san halin da xata shiga ba, kuma ni ina son matata, forgive me dad" kallonsa duk suka tsaya yi da mmki, dad yyi murmushin takaici yace "hka kace koh?" Khaleel bae ce komae ba har lkcn yana rike da kansa, dad yace "gud, bani dukka makullan gidajena dake hannunka da documents dina," Khaleel ya gyada kai da kyar yace "toh" snn ya mike ya fice daga falon duk suka bi sa da kallo da mugun mmki, gida Khaleel ya koma, har lkcin Ashnaah bata tashi ba ya dauki duk kaddaran dad dinsa dake hannunsa a dakinsa, snn ya fito ya samu mai gadinsa ya basa cheque din dubu hamsin yace ya ja jari ya sallamesa don xae rufe gidan ne sanin gidan dad dinsa ne ba nasa ba, abubuwan da yasan xae bukata ya kwashe a dakinsa ya kai cikin mota, snn ya dawo dakin ya shiga tada Ashnaah a hnkli, bude ido tayi tana kallonsa, ya sakar mata murmushi yace "srry na tashe ki koh?" Dagota yyi ya dauki hijab dinta ya sa Mata snn suka fito ya kulle gidan, ita dae bin sa kawae take don jiri ne ke dibanta, mota ya bude mata ta shiga ya kulle snn ya xaga ya shiga motar ya fice daga gidan ya fito ya kulle gate din ta waje don har mai gadin ya wuce snn ya koma motan ya shiga ya tada ya nufi gidansu, bacci Ashnaah take daga xaunen da take cikin motar ko da ya isa kofar gidansu, hkn ya basa daman fita ya nufi cikin gidansu ya haura sama xuwa falon dad dinsa, ynda ya barsu hka ya same su, ya isa gaba ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 96..... A hnkli Khaleel ya shiga tada Ashnaah a cikin mota bayan ya shiga hotel din yyi masu bookn din daki ya fito, Ashnaah ta bude ido tana kallonsa, da ganinta kasan bacci ne ssae a idonta, ya kamo hannunta yace "Cum on wife mu je ki kwanta, I knw yhu need rest" da taimakonsa ta fito daga motar ta shiga bin haraban hotel din kawae da kallo, snn ta juya tana kallonsa, murmushi ya sakar mata ya nufi entrance din shiga hotel din yana rike da hannunta har lkcn, bin sa kawae take har suka shiga hotel din ya haura sama da ita, room din da aka bashi suka nufa ya tura kofar dakin suka shiga, hijab din jikinta ya cire mata ya shimfida kan neat bedsheet din da ke kan gadon dakin snn yace ta kwanta tayi baccinta, bbu musu ta kwanta shi kuma ya fita don shigo da abubuwan da yasan xa su bukata, ko da ya dawo har ta koma bacci, ya ajiye jakar hannunsa ya xauna gefen gadon a sanyaye ya dafe kansa da yyi masa nauyi yana tunanin abun yi ynxu, yes yana da 4.5 mlln a acc ynxu wat is he suppose to do, idan yace xae siya gida there will b nothin left he knw, to da me xae kula da ita da bbyn da ke cikinta idan ya siya gidan, yes sae ya nemi aiki to meet up their needs nd demands idan ya siya gidan ynxu, kmr wnda ya tuno abu ya girgixa kai a hnkli ya lumshe ido yace "No! lookn 4 job is a kinda hell ynxu, dafe kansa ya kuma yi a xuciyarsa yace "its better I rent an apartment, yes 5 to 6 hndrd thousand I guess" shiru yyi yana tunanin shawaran da ya ba kansa na karshe, ajiyar xuciya ya sauke ganin hkn kadae ne abun yi ynxu, wayarsa dake gefensa ya shiga ring ya daga da sauri ya sa cylnt don kar ya tada Ashnaah, ya ga Najeeb ne ke kiransa, da kmr baxae daga ba don wani mugun haushinsa yake ji, sae kuma ya daga yace "ya aka yi?" Daga daya bangaren Najeeb yace "kana gida ne? Gani nn xuwa ynxu." Khaleel yace "bana gida ina Zaria, Akwae matsala ne?" Najeeb yace "of course no dan bakar mgna, kawae naga kwana biyu bamu hadu bne" Khaleel yace "ina Zaria ynxu, sae na dawo." Najeeb yace "ok ka kirani idan ka dawo" Khaleel yace "OK" snn ya katse kiran ya ajiye wayarsa tare da jan tsaki, ko kadan baya bukatan taimakon kowa a ynxu dae. Mikewa yyi ya fita don siyo mata abinda xata ci kafin ta tashi duk da yasan ba abincin ma take ci ba, wani supermarket ya tafi ya siyo kayan tea ya dawo snn ya siya abinci a eatry din dake cikin hotel din ya haura sama, xaune ya sameta kasan dakin ta hade kai da gwiwa, ya karaso ya durkusa gabanta a hnkli yace "me ya faru wife" ta dago kai tana kallonsa da kyar tace "amae nake ji," dagota yyi yace "mu je kiyi toh" kmr xata yi kuka tace "ya ki fitowa" xaunar da ita yyi gefen gado ya ce "idan kin ci abinci xae fito, ga abinci nn na siyo maki ki ci kadan sae kiyi aman" haransa tayi sae kuma ta saka kuka irin ta shagwaba, yyi shiru yana kallonta lkci daya yyi murmushi ya rungumota a hnkli yana shafa bayanta yace "to ya kike son in maki wife" lamo tayi a jikinsa bata ce komae ba, ya dago kanta yana kallon cikin idonta yace "to xa ki sha tea?" Ta make kafada alamar A'a, murmushi ya kuma yi yace "to me xa ki ci?" Kmr xata yi kuka tace "ni amae nake ji" mikewa yyi ya dauko ledan abincin da ya siyo ya dawo gabanta ta mike da sauri ta bar wajen don ko ganin abincin bata son yi, can karshen gadon ta koma ta xauna, ya ajiye abincin ya bi ta ya xauna gefenta yace "toh xa ki sha kunu?" Juyawa tayi tana kallonsa tayi shiru kmr me naxari snn ta gyada masa kai da sauri, wayarsa ya dauka, ya shiga neman layin Zeenat, har ya mance rabon da suyi waya, duk da da can ma ita ke kiransa ba shi ke kiranta ba, bugu daya ta dauka, suka gaisa tace "ka mance da ni ko doctor" Khaleel yace "A'a ban mance ki ba, ya mutanen gidan?" Zeenat tace "duk suna lfya, ya su Fateema da khadija" Khaleel yace "suna lfya, kina kd ne?" Tace "ehh ina nn" juyawa yyi yana kallon Ashnaah da ta hade rae tana kallonsa, ya mike ya fice daga dakin, sae bayan da ya fita yace "favour daya nake son kiyi min Zeenat" tace "na me fa Dr" Khaleel yace "kunu xa ki dama min plss idan bbu takura" da mmki Zeenat tace "kunu?" Yace "yeah pls" tace "to shknn office xan kawo maka?" Khaleel yace "No idan kin gama ki kirani kawae xan xo in amsa" tace "to shknn xan yi ynxu" yace "am grateful, ki hada min da ruwan xafi a flask plss" tace "OK bbu matsala" ya kuma yi mata gdya, snn ya katse wayar ya dawo dakin, karasowa yyi kan gado ya xauna gefen Ashnaah ganin ynda ta wani hade rae ta juya baya yace "me ya faru wife?" Kmr jira take "ta fashe da kuka tace "ina ruwanka," ya dan yi shiru snn yace "Allah ya ba ki hkuri wife" kmr ya kara tunxurata ta kuma rushewa da kuka, yyi murmushi ya mike jin ana kiraye kirayen sllhn magrib ya nufi bathroom, mikewa tayi da sauri ta nufi inda ya ajiye wayarsa ta dauka ta shiga call log don ganin da wnda ya gama waya, ajiye wayar tayi a sanyaye ganin Zeenat, ta koma inda take ta xauna duk gaba daya sae ta nemi aman da take ji ta rasa. Ko da ya fito kallo daya yyi mata ya fita daga dakin don xuwa masallaci, kasa tafiya masallacin yyi ya dawo dakin ya sameta ta sakko kasa ta hade kai da gwiwa tana kuka, ya karaso kusa da ita yana murmushi ya durkusa gabanta ya dagota a hnkli yace "I only belong to yhu wife, no one else but yhu" xaunawa yyi a hnkli ya jawota jikinsa yana murmushi. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar97.....Khaleel ya dago kanta yana kallon manyan idanuwanta murya can kasa yace "let me go nd praywife" sunkuyar da idonta tayi bata ce komai ba ya mike ta bi sa da kallo har ya fita daga dakin snn ita ma ta mike tsaye da nufin shiga bathroom tayi alwala taji baxata iya ba ta koma gefen gado ta kwanta, da kyar ta iya mikewa daga karshe ta shiga bayin tayi alwala ta fito ta dauki darduman da ta gani a dakin, har Khaleel ya shigo dakin bata idar dasllhn da take ba don duk sae da ta rama sallolin da ake binta, tana idarwa tayi kwanciyarta kan darduman don jiri kawae take gani, Khaleel ya dawoinda take yana kallonta yace "sannu wife" dauke kanta tayi bata ce komae ba, wayarsa dake hannunsa yyi vibrate ya daga tare da sallama, daga daya bangaren Zeenat tace "Na gama ya Khaleel" Khaleel yace "OK to gani nn tahowa" ajiye wayar yyi yana kallon Ashnaah yace "bari in je in dawo ynxu wife" Ashnaah ta mike xaune da sauri ta hade rae tace "ni xan bi ka" yace "to mu tafi" kasa tashi tayi daga xaunen da take, shi dae kallonta kawae yake, can yyi murmushi ya dagota ya dauki hijab dinta ya sa mata snn ya kama hannunta suka fita daga dakinya rufe kofar, sae da suka bar haraban hotel din Ashnaah tace "me yasa ka kawo ni Motel?" Khaleel yyi shiru kmr baxae bata amsa ba sae kuma a sanyaye yace "gobe xa mu tafi gida," kallonsa kawae Ashnaah ke yi bata dae ce komae ba, bakwae da rabi suka isa kofar gidansu Zeenat, Khaleel ya dauki waya ya kirata yace gashi ya xo, baa dau lkci ba ta fito rike da babban leda me dauke da flasks biyu, Khaleel ya fita ya sameta suka gaisa kuma snn ta mika masa ya karba yyi mata gdya yace "xo ku gaisa da Fateema tare mu ke" Zeenat tace "OK" snn ta nufi motar, Khaleel ya bude mata, da fara'arta ta gaida Ashnaah, bbu yabo bbu fallasa Ashnaah ta amsa mata, Zeenat tayi masu sae da safe snn ta koma ciki, Khaleel ya tada motar yana kallon Ashnaah da mood dinta ya gama canxawa, reverse yyi suka bar anguwan, sae a snn yace "y datface wife" Ashnaah ta dauke kanta kawae, wani bank taga yyi parkin yace "ina xuwa" bata tankasa ba ya fita ya nufi gun atm machine, ba a dau lkci ba ya dawo suka bar gun ya nufi wani boutique nn ma yyi parkin yana kallonta yace "ina xuwa wife" nn ma bata ce komae ba ya fita, ya kusa minti sha biyar a ciki snn ya fito, duk ta gaji gun kwanciya kawae takenema ga amae dake damunta ssae, back seat ya bude ya xuba ledojin hannunsa snn ya xaga ya shiga driver seat yana kallonta yace "ki yi hkuri wife kin gaji ko" tada motar yyi suka bar wajen. Yana gama parkin cikin hotel din ya fito ya bude mata motar ya kamo hannunta ta fito ya ji jikinta yyi xafi, da damuwa yace "ina ke maki ciwo ynxu" durkusawa yaga tana neman yi don bata jin xata iya tsayuwa, ya dagota xae dauketa ta girgixa kai da sauri tace "A'a ni bna so" kyaleta yyi yace "to mu shiga" ta shiga binsa a baya kanta na juya mata, dai dai stairs ta kasa ci gaba da tafiyar ta durkushe wajen, Khaleel ya dagota ya dauketa kawae ya karasa dakinsu da ita, kwantar da ita yyi kan gado, ta mike xaune murya can kasa tace "wanka xanyi" ya mike ya shiga bayin dakin, ko da ya fito kwance ya sameta, da taimakon sa ta cire rigar jikinta ta barves da skirt din jikinta, snn ta mike ya dauki towel dinsa ya mika mata ta shiga bathroom din da sauri, ruwan dumi ta samu ya tanadar mata da sabulunsa me ddin kamshi ga shower gel, a daddafe ta gama wankan ta daura towel amma ta kasa fitowa, hka kawae taji tana kunyansa ga shi bata shigo da hijab ba, ta fi minti biyar jingine jikin bango daga karshe ta ji tana neman faduwa ta fito rike da kayan da ta cire, bata samesa cikin dakin ba, ta ji ddi ssae ta isa inda hijab dinta yake da sauri ta dauka ta sa, kayan bacci ta gani a ajiye gefen gadon da turarurruka, ta tsaya kallon kayan snn ta karasa ta daga red silky gown din ta ga har da undies, kallon gown din kawae take, iyakar sa tasan baxae wuce cinya ba, gashi yyi mugun haduwa, ta tabe baki ta dauki underwear din ta koma bayi ta sa snn ta fito, tayi niyyar sllhn isha amma ta ji baxata iya ba hkn yasa tayi kwanciyarta har lkcn tana daure da tawul sae hijab a jikinta, ko minti biyar ba ta yi da kwanciya ba Khaleel ya shigo, ya ajiye abubuwan hannunsa ya karaso yana kallonta yace "tashi in xuba maki kununki sha" bae jira me xata ce ba ya fiddo wani sabon cup snn ya bude flask din kunun ya xuba mata da taimakon sa ta sauko daga kan gadon ya mika matakunun, ba musu ta karba tana kallon kunun, a hnkli ta kai cup din bakinta ta shiga sha don bbu xafi ssai,har sae da ta kusa rabi snn ta ajiye cup din tana goge bakinta, yace "kin koshi?" Kai ta gyada masa yace "aa dan kara kadan wife" girgixa Kai tayi ta shiga kkrin mikewa ya rikota yace "kadan fa xa ki kara" kuka ta sakar masa irin ta shagwaba, ya rungumota da sauri yace "A'a yi hkuri wife" kwantar da ita yyi ya dauki sauran ya shanye snn ya fiddo magungunanta ya dawo gefenta ya xauna yana kallonta xae yi mgna wayarsa da ke aljihunsa ya shiga vibrate, ya ciro yana kallon screen din ya ga umminsa ce ke kiransa, ya daga kiran, yyi mata sallama suka gaisa, Ummi tace "ya jikin fateemar?" Yace "da sauki Ummi" tace "ba ta mu gaisa idan tana kusa" kallon Ashnaah yyi ya mika mata wayar yace "ga shi ku gaisa da Ummi," ta mike xaune ta jingina jikin gadon ta karbi wayar tare da yin sallama, Ummi tace "ya jikin fateema? Kina cin abinci dae koh?" Ashnaah ta gyada mata kai tace"ina ci Ummi" Ummi tace "to Allah ya sauwake, ba shi wayan" Ashnaah tayi mata gdya snn ta mika masa wayar, Ummi tace "kuna ina ne ynxu Khaleel" Khaleel ya dan yi shiru snn a hnkli yace "muna gidan wani frnd dina ne Ummi" Ummi tace "kana ji na koh?" Yace "ina ji Ummi" tace "gobe dad din ka xae kira ka akan cewa ka ba shi takardun makarantar ka, I mean ur certificate don yana takaman he made yhu get it, toh kar ka kuskura ko me xae faru ka bashi, ka dae ji abinda na gaya maka koh?" Khaleel yyi shiru ya ma rasa me xae ce mata, a hnkli yace "shknn Ummi, na ji" ya fadi hkn ne kawae ba don baxae ba sa ba idan ya bukaci hkn,Ummi tace "Allah maka albarka" a sanyaye yace"Ameen" snn tayi masa sallama ta katse kiran, Khaleel ya daga kai yana kallon Ashnaah, ita ma kallonsa take, mikewa tayi da kyar har lkcn tana kallonsa murya can kasa tace "tel me wat is happenin plss" Khaleel ya sakar mata murmushi yace "tel me ya ku ka yi da parent din ki tukun?" Nanda nn hawaye ya cika idonta ta sunkuyar da kanta sae ga hawayen, dago kanta yyi a sanyaye yace"ban ce kiyi kuka ba wife" gyada masa kai tayi tana share hawayen fuskarta a hnkli tace "my dad disowned me, ya ce ya cire ni cikin ya yansa" kuka ssae ta fashe da, ya rungunmeta a hnkli shi ma yace "same wit me" dago kai tayi tana kallonsa, a hnkli ya shiga bata lbrin ynda su ka yi da Abbansa, Ashnaah ta fashe da wani sabon kukan, ya jawo ta jikinsa yace "its OK dear, Allah na tare da mu" kai kawae ta gyada masa, ta xame jikinta daga nasa ta kwanta, lallabata yyi ya bata maganin da ya dauko ta sha da kyar, snn ya mike yana kallon kayan baccin kan gadon snn ya kalli abinda ke jikinta yyi murmushi yace "baki canxa kaya ba" yi tayi kmr bata ji sa ba, yace "toh give me my towel, xan shiga wanka" mikewa tayi ta xaune kmr xata yi kuka tace"to sae in sa me?" Ya ce "ba ga kaya ba na siyo maki" ta wara manyan idonta tare da galla masa harara tace "wnn ne kaya?" Dariya yyi yace "to ae irinsu naga kike sa wa a can gidanmu, ko kin manta ne?" Ashnaah ta xaro ido tace "ni?" Ya karaso kusa da ita ya xauna yana mata wani irin kallo yana rike da rigan baccin yace "deny it, ba ki da irin wnn rigan," rufe fuskarta tayi da tafin hannunta da sauri, yyi dariya ya cire hannun, snn ya cire hijab din jikinta a hnkli yace "tashi ki sa kayan ki cire min towel dina" fixge hijab din tayi daga hannunsa kmr xata yi kuka tace "ni kunya nake ji" ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 98..... Tsayawa kallonta Khaleel yyi yana murmushi, ta mike a hnkli xata bar wajen ba tare da ta bari sun hada ido ba, rikota yyi da sauri ya xaunar da ita kan gadon yace "da gske kunya ta kike wife" sunkuyar da kai tayi, yyi murmushi ya shiga kwance tawul din dake jikinta a hnkli, ta wara ido ta rike da sauri tana kallonsa kmr xata yi kuka tace "don Allah ka bari" fingers dinsa biyu ya daura kan lebbenta alamar tayi shiru, a hnkli ta sauke idonta daga kallon da take masa, bata kuma hanasa ba har ya cire towel din daga jikinta ya dauki rigar baccin ya sa mata da kansa, ita dae bata bari sun hada ido ba don dauke kanta tayi cike da jin kunyansa, yana gama sa mata kayan ya kwantar da ita kan gadon, ta lumshe ido da sauri kmr me bacci ta juya masa baya, yyi murmushi ya mike ya nufi bathroom rike da towel din. Ko da ya fito Ashnaah tayi bacci, ya dde tsaye yana kallonta wani mugun sonta na fixgarsa, memory din ran da ya fara ganinta ya shiga dawo masa, gefen gadon ya xauna a hnkli yana murmushi "one early Monday Mrnin, yana xaune gun masu gyaran mota, ana duba masa motarsa, yes sae ga ta ta taho, ta burgesa a lkcn kuwa??" Ya girgixa kai yana ci gaba da murmushi "nop, not at all, hasali ma haushin distractin din shi da takalmin kafarta yyi ya ji a lkcn, yes tana sanye da atamfa somethin Ash da ratsin orange nd brown if he recalled well, handbag brown takalmi brown, hijab...." Murmushi yyi ssae don bae manta ba sarae, yasan kuma baxae taba mantawa ba a rayuwarsa, nd finally d receipt nd imprtnt documents dat cause ol dis," a hnkli ran da ta maresa ya fado masa, ya juya yana kallonta, murmushin nn dae ya kuma yi snn ya Mike don bae son ya kuma tunawa, jallabiyarsa ya saka snn ya shimfida darduma yyi shafa'i da wutr, ya dde xaune kan darduman yana tunanin situation din da ya tsinci kansa a yau, a whole him MD Ibrahim Khaleel, no job no home, murmushi yyi ya gode Allah snn ya mike ya kashe wutan dakin yyi kwanciyarsa gefenta, kasa bacci yyi daren ranan hkn yasa ya Mike ya kuma dauro alwala ya shiga sllh, sae kusan uku saura ya sallame ya dawo kan gadon yana kallon Ashnaah da ke ta juye juye, taba jikinta yyi yaji xafi, ya dagota ya rungumeta a hnkli yace "ina ke maki ciwo" ta bude ido ta girgixa masa kai da kyar tace "amae nake ji" shafa bayanta ya shiga yi a hnkli yace "xae daina wife" sun fi minti goma a hkn har ya ji alamar ta koma bacci snn ya kwantar da ita ya kwanta gefenta, birginowa tayi ta dawo ta shige jikinsa, ya lumshe ido ya rungunmeta ssae, ba a dau lkci ba ta kuma komawa bacci, sae a snn shima yyi baccin. Da Asuba Khaleel ya tashi, ya dde xaune kan gadon daga karshe ya mike ya shiga bayi don yin alwala, tashin Ashnaah yyi kafin ya fita xuwa masallaci, ta bude ido tana kallonsa, yace "ki daure kiyi alwala kiyi sllh wife," mikewa xaune tayi, yace "bari in tafi masallaci" ta gyada masa Kai snn ya fita, da kyar ta mike ta shiga bayin ta dauro alwala snn ta fito, tana idar da sllhn ta shiga bude ledojin da ta gani a dakin ko xata ga toothpaste da brush don kunu kawae take son sha, ta ga duk yawanci kananan kaya ne da ya siyo Mata, a wani ledan ta ga brush biyu da MacLean ta dauka ta shiga bayi ta wanke bakinta, a nn ta samu yin aman da take ji tun jiya, sae a snn taji ta samu relief duk da ta galabaita ssae, ta kuma wanke bakinta ta fito jiki ba kwari, dauraye cup din jiya tayi ta xuba kunun ta shiga sha, kadan ta rage ta ajiye, ta jinginar da kanta jikin gadon, Khaleel ya shigo dakin yana kallonta yace "kin yi sllhn wife?" gyada masa kai kawae tayi, ya kalli cup din dake kasa yace "kin sha kunun ne kuma?" Nn ma kai ta gyada masa ta kwanta don bata son mgna, nn da nn bacci ya dauketa, har Karfe goma bata tashi ba, hkn yasa ya shirya kawae ya fita nema masu apartment ko xae su samu a ranan. Sha daya saura Khaleel ya dawo, har lkcn Ashnaah bata tashi ba, ya dde tsaye yana kallon kyakkyawan surarta, snn ya karasa kusa da ita cike da kasala yana kallonta, first nyt dinsu tare kawae yake tunawa, yyi murmushi ya xauna gefenta ya shafa cikinta yana kallon fuskarta, a hnkli ya daura lips dinsa kan cikinta ya lumshe ido murya can kasa yace "babyna na sa ki bacci da yawa ko wife" bude ido tayi tana kallonsa, ya mike xaune da sauri, ya sakar mata murmushi yace "kina jin yunwa?" Girgixa masa kai tayi, xae yi magana wayarsa ya shiga ring ya dauka yana kallon me kiransa, gabansa ya fadi ganin Abbansa, kasa dagawa yyi ya ajiye wayar har ya katse, ya daga kai yana kallon Ashnaah da ke kallonsa, ya mata murmushi ta sunkuyar da kai, kuma kira aka yi, Khaleel ya juya yana kallon wayar a sanyaye, Al- ameen ne ke kiransa wnn karan, ya dauki wayar ya daga jiki ba kwari yyi masa sallama, gaisawa suka yi snn Al-ameen yace "kana gida koh Khaleel" Khaleel ya dan yi shiru snn ya girgixa kai yace "A'a bana gida" Al-ameen yace "OK ina xa mu hadu, i need ur informations, wani aminin dad dina ke neman qualify Dr da xae dinga runnin masa clinic dinsa, I guess ka ma san shi dad din Ahmad ne, yhu knw Ahmad ne ke runnin din clinic din toh he is goin abroad, d only prblm here is dat a Abuja ne, ko da yake ma wnn ba matsala bne a gani na, where will we meet ynxu?" Khaleel da tun fara mgnr abokin nasa yyi shiru, ya sauke ajiyar xuciya a sanyaye yace "bana kusa ynxu, if am bck xa mu yi waya" Al-ameen yace "OK I will b expecting ur cal" ajiye wayar Khaleel yyi ya dafe kansa, Ashnaah da ke kallonsa har lkcn a hnkli tace "me ya faru" ya dago kai yana kallonta lkci daya ya sakar mata murmushi don baya son yana nuna damuwansa gabanta yace "nothin wife just thinking" ita ma murmushin tayi ta sunkuyar da kanta, wayar da ya ajiye ya kuma ring yana dubawa ya ga dad dinsa ne kuma, kasa kin daga wayar yyi ya daga a sanyaye tare da yin sallama. Like · 7 · Reply · Report · 17 minutes ago ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar99......Shiru Khaleel yyi yana sauraren dad dinsa har ya kaikarshe ya katse kiran don kansa, runtse ido Khaleel yyi ya kasa ajiye wayar maganganun dad din nasa nae masa yawo a ka, lkci daya ya bude idon a hnkli yana kallon Ashnaah ya ga kallonsa take, murmushiya kirkiro tare da ajiye wayar, ta sunkuyar da kanta, murya can kasa tace "ka ba shi kawae doctor, he is a father....." Kasa ci gaba ta yi nn da nn hawaye ya cika idonta, Khaleel yyi mmkin ynda ta ji abinda dad dinsa ya gama fadi, ko da yake ba abun mmki bne ba ma idan ta ji ko don ynda dad din nasa ke daga murya, mikewa yyi bae ce komae ba ya nufi bathroom, Ashnaah ta bi sa da kallo, yana shiga ya hade kai da bango kansa na juya masa, y him? Hawaye ya ji ya cika idonsa, Ashnaah kam hade kai tayi da gwiwa ta shiga rera kuka a hnkli, a hka Khaleel ya fito ya sameta, ya karasa gadon a sanyaye ya dago ta a hnkli yana kallonta, kin bari su hada ido tayi, Khaleel ya rungumeta, yana kkrin mayar da nasa hawayen kar ta gani yace "its OK wife, Allah na tare da mu" ta kwantar da kanta a kirjinsa har lkcn hawaye na sakko mata bata ce komae ba, sun fi minti goma a hka, ta xame jikinta ahnkli daga na sa ta koma kan gado ta kwanta, Khaleel ya mike jiki ba kwari ya dauko briefcase dinsa ya shiga fiddo important documents din da dad dinsa ya bukata ya xuba su a envelope snn ya ajiye gefen gadon ya xauna yana kallon Ashnaah, a hnkli tace "wayata fa? I want to cal my mum" mikewa Khaleel yyi ya nufi inda ya ajiye mata wayarta tun jiya ya dauko ya mika mata, mikewa xaune tayi bayan ta karbi wayar ta ga miscals kusantalatin, dubawa tayi da sauri ta ga duk na momynta ne da Ashfah, da sauri ta shiga kiran layin mum dinta, bugu daya ta dauka, momy tace "Fateema" daga jin ynda ta kirata kasan tana cikin tashin hnkli, Ashnaah ta amsa a sanyaye tare da gaidata, momy tace "ina kika bar wayan ina ta kira, kina ina ynxu?" Ashnaah tace "a cylnt wayar yake momy, ina gida" momy tace "gidan mijin ki?" Ashnaah ta gyada kai a hnkli tace "eh momy" momy ta sauke ajiyar xuciya tace "to ya jikin naki" Ashnaah tace "da sauki momy"momy tace "to shknn ki dinga barin wayar kusa da ke sbda in ke samun ki" Ashnaah tace "toh momyna Ashfah fa?" Momy tace "tana kasa, kina dae cin abinci koh?" Ashnaah tace "ina ci momy" momy tace "to shknn xan kira ki anjima kin ji" Ashnaah ta ce "to momy" a sanyaye Ashnaah ta ajiye wayar, Khaleel ya dauki envelope din da ya ajiye gefen gado yana kallonta a hnkli yace "I will b bck right away sis" ta gyada masa kai ya fita daga dakin. Khaleel na isa gidansu ya nufi falon dad dinsa ya gaishesa da ladabi snn ya ajiye masa envelope din gabansa yyi masa sallama ya fita daga dakin, xauneya samu kanwarsa a falo, ta mike a sanyaye tana kallonsa tace "kayi hkuri ya Khaleel..." Hawaye ta shiga yi ta kasa ci gaba, ya gyada mata kai yace"Ummi fa" ta girgixa masa kai tace "ta fita" yace "OK kar kice mata na xo gun Dad" kai ta gyada masa, ya juya ya fice daga falon, yana drivin kiran Najeeb ya shigo wayarsa, ya share kiran har ya katse, aka kuma kira, sae da ya kira fiye da sau biyu snn Khaleel ya daga, Najeeb yace "wae me ke faruwa Khaleel, ynxu dad dinka ya kirani, look kana ina plss a ina xa mu hadu" Khaleel yace "bana gari" bae jira cewarsa ba ya kashe wayar gaba daya, sae da yyi sllhn Azahar snn ya shiga hotel din, bacci ya tarda Ashnaah ke yi, ya shiga bathroom don yin wanka. Karfe uku da kusan rabi yana xaune yana danna laptop har lkcn Ashnaah na bacci, wayarsa da ya kunna a lkcn ya shiga ring ya dauka yana kallon me kiran nasa ya ga Al-ameen ne, daga kiran yyi Al-ameen yace "wae baka dawo bne har ynxu Khaleel, or re yhu nt interested, if yes ae da gaya min kawae kayi ba wae ka share ni ba" Khaleel ya sauke ajiyar xuciya yace "kana ina ynxu mu yi mgna?" Al-ameen yace "ina gidana mana" Khaleel yace "OK toh xan xo anjima" sallama suka yi Khaleel ya ajiye wayar. Bayan magrib Khaleel ya kuma kiran Al-ameen, yace "Madam dinka na nn kd ne ita ma" Al-ameen yace "ehh tare muka xo" Khaleel yace "OK ga ni nn xuwa ynxu" ajiye wayar Khaleel yyi ya juya yana kallon Ashnaah da fitowarta daga wanka knn, ya mike ya dauko mata yar gown doguwa mara nauyi da ya siyo mata, kin saka kayan tayi a gabansa, ta dauki rigan da lotion din da ya ajiye mata ta koma bayi, shi dae bae ce mata komae ba, ta gama ta fito ta dauki hijab dinta da sauri ta sa don gown din is vry transparent, yyi murmushi ya dauki makullin motarsa da ledan flasks din da Zeenat ta kawo masu, don ta shanye kunun, ya juya yana kallonta yace "mu je toh" ba musu ta bisa suka fita ya kulle dakin snn suka saukakasa, bakwae da kusan rabi suka isa gidan Al-ameen, yyi horn mai gadi ya bude gate din ya shiga yyi parkin ya fito ya xaga don bude ma Ashnaah, Al-ameen ne ya fito daga cikin gidan ya karaso yana ma abokin nasa sannu da xuwa, da mmki yake kallon Ashnaah don duk tunaninsa har ynxu basa tare, Al-ameen yace "A'a ashe tare da amarya ku ke?" Khaleel yyi murmushi suka gaisa daabokin nasa, Ashnaah ma ta gaishesa snn suka nufi cikin gidan, Maryam ta ji ddin ganin Ashnaah ssae, ta haura sama da ita xuwa dakinta, sae a snn Al-ameen ya juya yana kallon abokinsa yace "ashe dae an baka matarka frnd, amma baka da kirki kai din nn, irin ban kai matsayin in sani ba din nn koh" Khaleel ya dan yi murmushi bae ce komae ba. Hkn yasa Al-ameen ma yyi shiru, a nutse Khaleel ya faragaya ma abokin nasa ynda suka hadu da Ashnaah har ya aureta da irin abubuwan da suka dinga faruwa tun da ya aurota har xuwa ranan da Ashnaahta ga takardan saki a dakinsa ixuwa ynxu da suke xaune, kallonsa kawae Al-ameen yake da mmki ssae, can ya girgixa kai cike da tausayi abokin nasa yace "toh wat did ur so called frnds did about this?" Khaleel ya dan yi murmushi yace "Najeeb kawae yasan halin da nake ciki cikin frndz dina" Al-ameen yace "then wat help did he rendered yhu?" Khaleel ya girgixa kai ya gaya masa ynda suka yi da Najeeb da ya xo gida ya same shi na karshe, Al-ameen yyi tsaki yace "wllh wllh wnn gayen da kke bi ba aboki bne," Khaleel dae yyi shiru bae ce komae ba, Al-ameen yace "ynxu me kke tunanin ya kamata ayi,ni baka gaya min komae bare in dinga ba ka shawara Khaleel" Khaleel ya girgixa kai da damuwa yace "I donno, am so confuse frnd, but kasan me yasa hnkli na bae wani tashi ba, ummina bata fushi da ni she understand me well dat's y nake da rest of mind" Al-ameen ya girgixa kai yace "ka tsaya kayi tunani da kyau Khaleel kuma ka gaya min gskyar ka,ka taba mgnr xaka saki matarka gaban kowa, I mean frnds hka" Khaleel yyi shiru snn yace "da Najeeb kadae na taba irin wnn mgnr, bn taba da kowa ba bayan shi" Al-ameen yace "kuma sae yace maka me a lkcn?" Khaleel yace "ya kan ce in saketa kawae in huta" Al-ameen ya dan yi murmushi yace"to xaka iya tuna wnda ya dawo da kai gida da ka je birthday ka sha ruwan naku," Khaleel ya dan yi murmushin da bae shirya yi ba yace "I knw Najeeb ne xae kawo ni gida ko faruqh duk da ban ma bukaci sanin wnda ya maido ni ba" Al-ameen yyi shiru snn yace "kuma kace kafin ka fita cikin drawern ka dauki wristwatch baka kuma ga takarda ba a lkcn koh" Khaleel ya gyada masa kai, Al-ameenyace "just tel me meyasa ka fi tunanin Khadija ce ta saka takardan cikin drawern ka, nt ur sily frndz?" Khaleel yace "coz duk duniya ita kadae xata yi rubutu exactly irin nawa, none of my frnd will do dat to me" Al-ameen yace "shknn gobe xan je in samu Ameeshan....." da sauri Khaleel yace "No, plss ka rabu da ita, me xaka je yi mata" Al-ameen yace "ni ynxu I only want to help my frnd nd bring bck his happiness once again, don hka ka xuba min ido kawae Ibrahim, stop questionin me" Khaleel yyi shiru yana kallonsa, ko kadan bae gamsu da xuwan abokin nasa gun Ameesha ba don shi ko sunanta ma bae son ji, Al-ameen yace "tashi ka tafi gun matarka nd check on her, tun da kace bata da lfya" mikewa Khaleel yyi, Al-ameen yyi masa jagora har xuwa dakin da Ashnaah take snn ya sauka kasa donMaryam na kitchen, Khaleel ya karaso cikin dakin yana kallonta yace "kina jin yunwa ko wife?" Dago kanta tayi da kyar tace "Amae" ya xauna gefenta ya rungumota yace "to kin ki cin komae bare kiyi aman wife"1 min·Khaleesat Haiydar...More Khaleesat Haiydar ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 100..... Ashnaah bata ce komae ba har lkcin yana rungume da ita, ya dago kanta yana yana kallon fuskarta a hnkli yace "to me kike son ki ci?" Girgixa masa kai tayi alamar baxata ci komae ba, kwankwasa kofar dakin aka yi, Ashnaah ta janye jikinta daga nasa da sauri, Maryam ta tura kofar dakin da sallama ta shigo rike da faranti dauke da kulan abinci da plates da drinks, ta karaso cikin dakin ta ajiye tana murmushi tace "amarya ga abinci" murmushin Ashnaah ta mayar mata, Khaleel yyi mata gdya ta fita ta kullo masu kofar, Khaleel ya sakko daga kan gadon ya bude kulan ya ga tuwon shinkafa ne da miyar vegetable, ya daga kai yana kallon Ashnaah ya ga ta boye fuskarta kan gadon alamar ko ganin abincin bata son yi, rufe abincin yyi ya dawo gefenta ya xauna yace "to me xa ki ci Fateema, baki ci komae ba tun safe fa" dago kai tayi a hnkli tana kallonsa kmr xata yi kuka tace "kila kunu xan sha, amae xan yi idan naga wnn" yyi shiru yana kallonta snn yace "to kar mu ba Maryam wahala, in kira Zeenat ta maki koh" gyada masa kai kawae tayi, ya mike ya fita falo don ya bar wayarsa can. Karfe tara da kusan rabi bayan Khaleel ya je gidansu Zeenat ya karbo ma Ashnaah kunu ya ce da Al-ameen xa su tafi, Al-ameen yace "ina xa ku?" Khaleel yace "hotel din da mu ke" Al- ameen yace "gidan nawa bae maka ba knn koh" Khaleel yyi murmushi yace "ba hka bne frnd kayan mu na can ne" Al-ameen yace "to ka je ka kwaso su ynxu, in kuma kafi son xaman hotel din ne to ka tafi ka karata amma ka bar matar ka nn," Khaleel yyi dariya yace "Alryt, tnx for accomodatin us frnd" Sun dde suna hira da abokin nasa a falo snn Al-ameen yace "ka ga ka tashi ka tafi gun wife dinka, ni ina nn har midnyt" Khaleel ya mike kmr jira yake don dama gaba daya hnklinsa yyi can yace "toh Allah ya ba mu alkhairi," ya nufi sama. Xaune ya tarda Ashnaah kan gado ta jingina jikin gadon, ya karaso da sauri yana kallonta yace "kin sha kunun da yawa wife" gyada masa kai tayi kawae, a hnkli tace "Cikina ke min ciwo" ya mike ya dauko wani ledan da ya shigo da daxu ya fiddo magunguna da allurori, ya shiga hada alluran, kallonsa kawae Ashnaah ta ke, ya lura da hkn ya dago kansa shi ma yana kallonta, kauda kai tayi da sauri cike da jin kunya, yyi murmushi ya ci gaba da abinda yake, har ya gama snn ya mike ya dawo inda take ya ce "a cinya xan maki koh" make kafada tayi kmr xata yi kuka tace "um um bna so" juyawa ya ga tayi ta kwanta tayi ruf da ciki, ya gane abinda ta ke nufi, yyi murmushi ya dawo inda take ya mata alluran, lallashinta ya shiga yi tun kan ta fara masa kuka don ya ga alamar hkn, ya dagota yana kallon hawayen idonta da yasa idon kyalli, jawota yyi jikinsa ya hade goshinsa da nata a hnkli ta ga ya lumshe ido, ko ba a gaya mata ba tasan me yake shirin yi, ta dauke kanta da sauri alamar bata so ta shiga kkrin kwace kanta, rungunmeta yyi ssae, a hnkli murya can kasa yace "plss wife" girgixa masa kai ta shiga yi kmr xata yi kuka tace "A'a bna so" ya daura bakinsa kan wuyanta kmr me rada yace "to na daina wife" Washegari karfe sha daya saura Al-ameen ya kama hanyar gidansu Ameesha kmr ynda ya ce, bae samu wahalan ganinta ba don sun fito knn da drivernta xae fita da ita, sakkowa tayi daga bayan motar tana kallon Al-ameen kmr tana son tuno inda ta san shi, Al-ameen yyi murmushi yace "Kin manta ni koh?" Shiru tayi bata ce komae ba, Al-ameen yace "By d way, sunana Al-ameen, abokin Dr Khaleel, na xo gun ki kuma sae ga shi xa ku fita" ssae ya ga jikinta yyi sanyi a hnkli tace "kayi hkuri bn gne ka ba, mu shiga daga ciki toh" juyawa tayi ta sallami drivernta a kan ta fasa fita, kallonta kawae Al-ameen yake cike da tausayinta gashi ta rame kan ynda ya Santa, ta juya tana kallonsa tace "mu shiga ciki" ba musu ya bi bayanta suka shiga cikin gidan, dae dae nn Hajiyarsu ta fito raka bakinta, da mmki take kallon yar tata tace "kaddae kin fasa fitan Meesha" Ameesha ta girgixa mata kai tace "A'a nayi bako ne" da mmki Hajiyar ke kallon Al-ameen don a iya saninta tunda Ameesha ta dawo gida daga gidan khaleel bata kallon duk samarin dake bibbiyanta, Hajiyar tayi murmushin jin ddi suka gaisa da Al-ameen duk a tunaninta sabon saurayi tayi don da tasan abokin Khaleel ne bbu shakka kaca kaca xata yi masa, don bbu ranan Allahn dae xae wuce da baxata yi ma Khaleel Allah ya isa ba. Karkashin daya daga bishiyoyin da ke compound din suka xauna, Gaishesa ta kuma yi, Al-ameen ya amsa yana tambayarta kwana biyu tayi murmushi bata ce komae ba, sae da aka dau kusan minti biyu snn Al- ameen yace "ki gaya min gskya khadija kar ki boye min komae, ke kika rubuta takardan nn ko ba ke ba?" Hawaye ne ya shiga bin kuncinta ta ma rasa abinda xata ce masa can ta fashe da kuka tana kallonsa, bae ce mata komae ba tayi mai isarta snn a hnkli tace "wllh bani ce nayi rubutun nn ba, don me ake tunanin xanyi hka, y will I do dat, me Fateema ta min xan mata hka, tun da na shiga gidan kallon bnxa bae taba hadani da ita ba kuma ni na dauketa tamkar kanwata da muka fito ciki daya, Khaleel bae min adalci ba da yyi tunanin xan iya yin hka" Al-ameen ya sauke ajiyar xuciya yace "ranan da ya je birthday wa ya maido sa gida" Ameesha na share hawayen da ke sakko mata tace "Najeeb" Al-ameen yace "falo ya shigo da shi ko waje ya bar sa" ta girgixa masa kai tace "har bedroom dinsa ya kai sa" Al-ameen ya xaro ido yace "bedroom" Ameesha ta gyada masa kai, Al- ameen yyi murmushi yana shafa gemunsa yace "kin bi sa dakin ne?" Ta girgixa masa kai a hnkli tace "har Washegarin ranan ban shiga dakinsa ba, Fateema kadae ce naga ta shiga da safe" Al-ameen yace "gud, bani digit din ki, xan wuce ynxu" wayarsa ya mika mata ta karba ta saka nmbrta snn ta mika masa, yyi mata gdya ya mike, ita ma hka, sallama yyi mata ya nufi gate, kasa daurewa tayi ta bi sa da sauri a sanyaye tace "Khaleel din fa" Al- ameen ya juya yana kallonta yace "yana nn, abubuwa da yawa sun faru bayan rabuwarku kar ki damu xa muyi waya idan na koma gida" gyada masa kai kawae ta iya yi hawaye cike idonta. Al-ameen ya juya ya fice daga gidan. Sha biyu Al-ameen ya isa gidansa, kofar gida ya tarda Khaleel jingine jikin wata mota da wani, parkin yyi nn kofar gidan ya fito don ganin shi da waye a tsaye, Najeeb ya ga ni, Al-ameen ya wani hade rae yana kallon Najeeb din, Najeeb ya daga kai yana kallon Al-ameen din, ganin irin kallon da yake masa yasa shi ma ya shiga masa wani matsiyacin kallo irin na yan duniya. Al-ameen ya girgixa kai tare da jan tsaki ya shige cikin gidansa, Najeeb yyi tsaki yace "wnn abokin naka dabba ne wllh, shi ba dan kowa ba sae girman kan tsiya, ko kadan bae san darajar dan Adam ba, kar ya raina min wayo don ya gan ni tsaye kofar gidansa" Khaleel dae bae ce komae ba sae murmushin da yyi, Najeeb ya mika masa makullin hannunsa yace "gashi nn na baka gidana na, U.rimi har komae ya dawo maka nml frnd dnt tell me no plss, snn don Allah ka je ka ba dad din ka hkuri he is jet angry at yhu, I will help yhu get bck ur document don dad dina ya sama maka aiki amma a Zaria, ka gaida min fateeman" Najeeb ya ciro Atm dinsa ya mika masa yace " take this ka siya duk abinda ka ga ya dace na kayan abinci idan kun tafi can gidan," ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar101.....Khaleel ya girgixa kai yana kallon Najeeb yace "kar ka damu frnd, hold on to ur atm, I have enuf...." Najeeb bae jira ya karasa ba ya kamo hannunsa ya saka masa key da atm din hannunsa ya juya ya shige motarsa ya tada yyi reverse, bin sa da kallo Khaleel yyi har ya bar anguwar snn ya sauke ajiyar xuciya ya juya ya shiga gida, falo ya tar da Al-ameen xaune yana danna waya, ya karaso cikin falon yana kallonsa xae yi mgna Al-ameen ya riga sa, "Me wnn mutumin ya xo yi a kofar gida na?" Khaleel ya xauna kan kujera yace "he came to check on me" Al-ameen ya Mike yace "duk ya kuskura ya sake xuwa kofar gidan nn sae na sa an daure shi wllh, kana nn makashinka na tare da kai baka sani ba, to wnn da kke kira da abokinka shi ya rubuta takardan da kke xargin matar ka ce ta rubuta,in ko ba shi ne ya rubuta ba to wllh ko rantsuwa nayibaxan yi kaffara ba da hadin bakinsa aka rubuta" Khaleel ya Mike shi ma yana kallonsa yace "haba! don ba ku shiri da shi bae kamata kayi masa irin wnn xargin ba Al-ameen, kasan ynda mu ke da Najeeb kuwa, gskya am nt happy with ur wordz, kawae don u re nt in gud terms da shi sae kayi masa wnn xargin, wnn kmr kaxafi ne kayi masa ma"Al-ameen ya girgixa Kai yana ma abokin nasa kallontausayi yace "vry soon xaka gane ko sharri nayi masa ko akasin hka" bae jira cewarsa ba ya nufi sama, Khaleel ya bi sa da kallo tare da jan tsaki, shi kam ya rasa me yasa Al-ameen ya ki jinin Najeeb hka, wani tsakin ya kuma ja ya nufi sama shima, xaune ya samu Ashnaah a kasan tiles din dakin ta jinginar da kanta jikin gado idonta lumshe kmr me bacci, ita kadae tasan abinda take ji, durkusawa yyi gabanta yana kallon ynda ta rame ssae sae hasken da ta kara, ta bude ido a hnkli tana kallonsa, ya daura hannu a goshinta ya ji xafi ssae hka ma duk jikinta, shiru yyi yana kallonta don ya san tana bukatar drip gashi kuma ba su yi settling ba tukun, murya can kasa tace "Doctor" shi ma murya can kasa yace "Wife" ta sunkuyar da kanta a hnkli tace"ka cire min cikin nn plss" tana fadin hka ta dago kai tana kallonsa hawaye cike idonta, xaro ido yyi lkci daya ya hade rae ya mike yace "wat? kina da hnkli kuwa?" Hawaye ne ya shiga bin kuncinta, yyi tsaki ya juya ya fice daga dakin, ta fashe da kuka a hnkli ta hade kai da gwiwa, gajiya tayi da kukan tayi kwanciyarta nn wajen, sae da aka yi Azahar snn ya shigo dakin da leda a hannunsa, ya ajiye ledan ya karaso gabanta ya durkusa yace "me yasa xa ki kwanta kan tiles?" bnxa tayi masa ta dauke kai, bae kuma tanka ta ba ya gama hada drip din da ya siyo ya makale shi snn ya mike yana kallonta yace "kina jin yunwa koh wife?" yi tayi kmr ba da ita ya ke ba, ya karasa kusa da ita ya dagota, ta sakar masa kukaya dauketa, duk ya ji ta fayau ba nauyi ya kwantar da ita kan gado ta mike xaune da sauri cikin kuka tace "bana so, ni ka kyaleni" murmushi yyi yana kallonta yace "to me nayi maki, ni kawae bbyna xan kara ma lfya fa?" Ta kuma fashewa da matsanancinkuka tana kallonsa, ya jawota jikinsa a hnkli yace "tosbda me kike son mu yi kisa wife?" Cikin kuka tace"sbda bna son cikin, kullum sae inyi ta jin amae, ko ina ya dinga min ciwo?" Khaleel yyi murmushi yace"toh shknn xan cire maki amma da sharadi," ta dago manyan idonta tana kallonsa, alamar ya gaya Mata sharadin, jin yyi shiru yasa a hnkli tace "na mene?" Yace "xan gaya maki anjima da daddare, ynxu dae ki bari in sa maki drip din don ki ji kwarin jikin ki kafin a cire cikin" wani irin kallo tayi masa sae kumata saka kuka tace "ka tsamman ni yarinya ce, wae nixaka ma wayo koh, to bana son drip din wllh, kuma da kaina xan je a cire cikin, don ba kai kke wahala ba shi yasa kke son ka mun wayo" kallonta kawae Khaleel yake can ya mike ya fice daga dakin. Bae kuma dawowa dakin ba har aka yi sllhn la'asar yana xaune falo da Al-ameen suna tattaunawa, Khaleel ya girgixa kai yace "he won't ever get me, bana ma son in je in kara bata masa rae" Al-ameen yace "kai dae ka gwada tukun Khaleel, dad naka fa na da saukin kai, parent dinta ne suka harxuka shi hka" Khaleel yace "OK I will do as yhu said, ita kuma natadad din fa ya xa mu yi da shi? Ya dau xafi da yawa" Al-ameen ya girgixa kai yace "may b idan ya ga grand child dinsa xuciyarsa xae yi sanyi, ko kuma idan gskya ta bayyana, amma kar ku je gun sa ynxu gskya" Khaleel yace "cikin da take cewa sae na cire mata ma" Al-ameen yace "ka share ta kawae, haukakke xa ka cire mata ciki, nd lastly Khaleel idan xa kaji ta nawa ka mayar ma da Najeeb duk abun da ya baka daxu, he is a crook, though u won't get dat now sae nn gaba idan komae ya bude, but sae in har xa ka ji ta nawa, idan taimakon ka yake son yi don me bae yi tun da ba sae da ya ji kana gidana, get this plss... Yhu went to birthday on dat vry day, u got drunk, ya maido ka gida ya kai ka har cikin dakin ka, sae ga shi washegarin ranan an ga takardan saki cikin drawern ka, kuma idan ba mantawa nayi ba jiya da kke bn lbri kace shi yace Fateema ta ba ka magani cikin drawern idan ka tashi, y will ur common sense nt make yhu understand somethin in here?" Shiru Khaleel yyi yana kallon abokin nasa maganan sa na karshe na masa yawo a ka, girgixa kai yyi a xuciyarsa yace "No! Najeeb baxae min hka ba, never! No he cant." Al-ameen sae kallonsa yake don for sure yasan Khaleel ba dauka xae yi ba, can ya tabe baki yace "no big deal, watarana in fact ba sae ma watarana ba vry soon gskya xata bayyana" Khaleel dae bae ce masa komae ba, Al-ameen yace"in ka ga xa ka iya tsayawa gidana gashi ku tsaya damatarka don gobe xa mu koma Zaria, I took a wk leave, nd tomorrow is makin it a wk, in kuma ka ga kafi son gidan Najeeb din ne fine," Khaleel dae bae ce komae ba Al-ameen ya dauki wayarsa da ake kira ya daga, mikewa Khaleel yyi ya nufi sama, ko kadan bae ji ddin xargin da Al-ameen ke ma Najeeb don a tunaninsa dat will be d lst thin da Najeeb xae masa a rayuwa" amae ya tar da Ashnaah ke yi a bathroom kmr xata amaye hanjin cikinta, ya karasa da sauri ya durkusa kusa da ita cike da tausayinta yana mata sannu, kuka ta fashe da, ya mike ya shiga gyara mata jiki snn ya fito da ita daga bayin, kwanciya tayi nn da nn baccin wahala ya dauketa, sae da daddare ya samu ya lallabata ya sa mata drip din bayan ta dan sha kunun da Maryam tayi Mata, hka ya kwana ranan yana gadinta da daddare don duk motsin da xata yi a kan idon sa, sae Asuba drip din ya kare ya cire mata, snn yyi sllh ya samu ya kwanta. Karfe goma saura na safe Al-ameen yace da Khaleel xa su koma Zaria, Khaleel ya kasa ce masa baxae xauna gidansa ba ya amsa da xae xauna kawae duk da bae yi niyar xama ba, dubu hamsin Al-ameen ya basa ya rike, Khaleel ya ki amsa yace ae yana da kudi enuf, nn kan centre table Al-ameen ya bar masa ya fice daga falon, Maryam ta so suyi sallama da Ashnaah amma har lkcn bata tashi ba, tace "in ta tashi ka ce mata sae mun yi waya doctor, kuma plss ka kula da ita da kyau, cikin nn na wahalar da ita wllh, da xa ka ji ta nawa ma kace momy ta samo maku yar dattijiwa da xata dinga kula da ita ta dinga mata duk abinda take so tun da na ga kunu ma kawae take iya sha" Khaleel yace "In'sha Allah Maryam, tnx a lot we re grateful" har bakin motarsu ya raka su, sae da Al-ameen ya ja masa kunne kan kar ya kuskura ya bar Najeeb ya kara xuwa kofar gidan snn suka wuce, shi dae Khaleel murmushi kawae yyi ya komacikin gida yana tunanin ynda xae tunkari dad dinsa, yasan ma ba sauraransa xae yi ba, yana shiga daki ya tar da wayar Ashnaah na vibrate ya dauka yana kallon mai kiranta, momy ya gani, yana rike da shi har ya katse ya ga miscals din da yawa kuma duk na momynta ne da Ashfah, kira aka kuma yi ya juya yana kallon Ashnaah da ke ta bacci, ya fara tunanin ya daga ko kar ya daga. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar102....Sae da wayar ta kusa katsewa snn Khaleel ya daga, shiru yyi da farko don ya rasa ta inda xae fara mgnan, jin momyn ta ambaci sunan Fateema yasa ya bude baki da kyar yyi mata sallama, shiru momy tayi daga daya bangaren, sallaman ya kuma yi momy ta amsa wnn karan, dukar da kai yyi kmr tanaganinsa ya gaisheta, momy ta amsa ta kuma yin shiru, rasa me xae kuma cewa yyi, can yyi saurin cewa "Amm bacci take momy, idan ta tashi xa ta kira" Momy tace "OK ngd" sallama yyi mata ta kashe wayan, Khaleel ya sauke ajiyar xuciya ya ajiye wayar ya xauna gefen gado yana kallon Ashnaah, wayarsa ya shiga ring ya daga yana kallonme kiran ya ga umminsa ce, ya daga tare da mata sallama suka gaisa, Ummi tace "Fateema fa? Ya jikin nata?" Yace "Da sauki Ummi, bacci ma take" Ummi tace "to Allah ya sauwake, dama Rukayya ce tace tana son xuwa, shine nace bari in kiraka ka fada mata inda kuke" Khaleel yace "to Bari in kirata Ummi" Ummi tace "toh shknn, ka gaida fateeman idan ta tashi" sallama suka yi ya katse kiran ya shiga neman layin kanwartasa don yi Mata kwatancen inda su ke. Yana ajiye wayar kiran Zeenat ya shigo wayar kuma, dagawa yyi suka gaisa tace "dama ina son xuwa in duba Fateema ne doctor" Khaleel yace "OK bbu damuwa, lemme sendyhu address" Address din gidan Al-ameen ya tura mata, Karfe sha daya Rukayya ta iso gidan ta kira shi, Khaleel ya fito ya tare ta su ka shiga gidan a tare, falo ta bar abincin hannunta da Ummi tace ta kawo ma fateema ya nufi sama da ita, a stairs yake tambayar ta ko dad dinsu na nan, tace "ya tafi Abujajiya," yace "OK, me kika kawo a kula" tace "waina ce da miya" Ashnaah na xaune suka shigo dakin, ta daga kai tana kallon Rukayya, Rukayya ta karaso inda take ta xauna gefen gadon tace "sannu, ya jikin?" Ashnaah tace "da sauki" Rukayya tace "to Allah ya kara lfya" mikewa tayi ta fita daga dakin don ba sabawa suka yi ba ta koma falo, Khaleel yace "Ummi ta kawo maki waina xa ki ci?" Shiru tayitana kallonsa, nn da nn ta ji sha'awar wainan sae dae tana tsoron kar ya sa ta amai, kmr xata yi kuka tace "nima bn san ko xan ci ba" murmushi yyi ya mike ya fita dakin, sae ga shi ya dawo rike da plate din wainar da miya a wani bowl, dauke kanta tayi dasauri ya karaso yace "baxa ki yi amae ba wife, dan kadan xa ki ci" a hnkli ta dago kanta tana kallon abincin, ya sakko da ita kasa yace "toh ci kadan ba da yawa ba" ta dan leka miyan ta dauke kai tace "ni hka xan ci bbu miya" yace "to dauka ki ci" daukan daya yyi ya kai mata baki ta karba ta shiga ci a hnkli,tun da ta fara laulayi sae ranan ta sa abinci baki, wayarsa ya dauka jin ana kiransa ya ga Zeenat ce, ya dauka tace ga ta a kofar gida, Rukayya ya kira yace ta je ta shigo da ita, Ashnaah tace "wacece?" Ya ajiye wayar hannunsa yace "Zeenat ce xa ta xo gaishe ki wae" ta hade rae tace "me ya same ni?" Yi yyi kmr bae ji ta ba, sae kuma yace "momy ta kira kidaxu kina bacci na dauka" Ashnaah tace "wace momy" ya daga manyan idonsa yana kallonta yace"ur mum" shiru tayi tana kallonsa, a hnkli tace "me kace mata?" Ba tare da ya kalleta ba yace "na ce kina bacci" wayarsa ya dauka ya mika mata yace"gashi ki kirata" ba musu ta karbi wayar a sanyaye, ya mike ya fita daga dakin, bugu biyu momy ta dauka, Ashnaah tayi mata sallama tare da gaisheta, momy tace "kina lfya fateema? Ya jikin?" Ashnaah tace "da sauki momy, kin kira daxu ina bacci" momytace "ehh, kina dae cin abinci koh?" Ashnaah ta gyada mata kai tace "ina ci momy, Ashfah fa?" Momy tace "dama ita ce ke damuna tana son xuwa gun ki, shine nace Bari in kira in gaya maki ki tura mata address" a sanyaye Ashnaah tace "Abba fa momy?" Momy ta dan yi shiru snn tace "baya nn, yana Abuja" Ashnaah tace "toh xan turo mata address din ta nmbrta" sallama suka yi Ashnaah ta ajiye wayar Khaleel, jikinta a Sanyaye, duk lkcn da ta tuna kalaman Abbanta na karshe a kanta sae ta ji hnklinta ya tashi, bata fatan Allah ya dauki ranta bata yi reconcile da Abbanta ba ya yafe Mata, da koh ta bani a rayuwa, hawaye ne ya shiga sakko Mata, dai dai nn Khaleel ya shigo dakin, karasowa yyi inda take da sauri ganin hawaye fuskarta da damuwa yace "me ya faru wife, momy ta ji haushi na daga kiranta koh?, am vry srry I won't do dat again" girgixa masa kai tayi tana hawaye a hnkli tace "bata ce komae ba, Abbana nake tunani" Khaleel ya dan sauke ajiyar xuciya yace "kar ki damu wife, wataran sae lbri, kuma In'sha Allah duk xa mu gama da iyayen mu lfya" gyada masa kae kawae tayi, yace "to share fuskar ki, kin ga Zeenat taxo gaishe ki" lkci daya Ashnaah ta hade rae tace"wae gaisuwar me xata xo ta min," Khaleel yyi shiru snn yyi murmushi, Ashnaah tace "bana son gaisuwar, ta wani xo wajen ka ta fake da cewar ni taxo gaisarwa meye hadi na da ita, ina ta san ni ko kuma na Santa, kawae ta xo wajen ka ta wani ce ta xo gaishe ni" fashewa da kuka tayi, Khaleel ya danne dariyarsa yace "Haba bby meye abun kuka a nn, ba sae in bar gidan ba idan ta gama gaishe ki ta yi wucewarta" Ashnaah ta galla masa harara ya mike yana dariya ya fita, bin sa tayi da kallo lkci daya ta ji haushin kanta, share hawayen fuskarta ta shiga yi a hnkli, y will she show she cares dat much abou him, he is d cause of everythin she is goin through, me yasa son sa ya shigeta lkci daya bayan duk wahalan da ta sha a hannunsa, girgixa kai tayi ta tura wainan gabanta cike da jin haushin kanta, dae dae nn Zeenat ta shigo dakin da sallama rike daflask a hannunta da ledan fruit, Ashnaah ta sunkuyar da kai da sauri, Zeenat ta karaso gabanta tana murmushi tace "sannu Fateema, ya jikin" Ashnaah ta kasa yi mata abinda tayi niya, ta dago kanta ta dan kirkiri murmushi tace "da sauki, Alhmdllh," Zeenat ta ce "toh Allah ya kara lfya, ga kunu na yo maki" Ashnaah tace "to ngdd Allah ya saka da alkhairi" Mintin Zeenat goma a dakin ta mike tace "xa ta koma" Ashnaah ta kuma yi mata gdya snn tace bari ta rakata falo, duk ynda Zeenat taso tayi xamanta ta bar rakiyan kn yadda Ashnaah ta yi suka sauko har falo, Zeenat na kallon Rukayya dake kallo a falon tace "doctor fa Rukayya?" Rukayya tace "ya fita wllh" Ashnaah na jin hka ta juya ta nufi sama, Zeenat tace "to idan ya dawo ki ce masa na tafi" Rukayya tace to, snn suka yi sallama ta fita, sae a snn hnklin Ashnaah ya kwanta ta koma sama, Karfe biyu saura Rukayya tayi ma yayanta da Ashnaah sallama ta wuce gida. Da yamma Karfe hudu da rabi Khaleel ya sa Ashnaah ta shirya suka tafi can gidansu tun da Abbansa na Abuja. Suna gidan har kusan Karfe shidda sae ga Abba ya dawo daga Abuja, ba karamin tashi hnklin khaleel yyi ba don bae taba xaton dawowan dad din nasa a lkcn ba, toh da wani idon ma xae kalli mahaifin nasa, da ma bae shigo da motarsa cikin gidan bne, ita kanta Ummi bata so dawowan mai gidan nata ba a lkcn sanin ita kanta sae ranta ya baci, ae kam hka ya faru don ko da ta je yi masa sannu da xuwa shareta yyi, ta bar masa dakinsa kawae, tana dawowa bedroom dinta Khaleel da ke xaune ya rike kansa ya mike da sauri yace "Ummi xa mu tafi" Ummi ya galla masa harara tace "tana baccin xa ku tafi" ya juya yana kallon Ashnaah da kebacci tun shigowar su gidan, a hnkli yace "tashin ta xan yi Ummi" Ummi tace "bbu inda xa ku sae ta tashi" kasa mata musu yyi ya koma ya xauna, ita kuma ta ci gaba da abinda take, a hnkli yace "xan iya xuwa gaida dad Ummi" girgixa masa kai tayi ba tare da ta kallesa ba tace "A'a kar ka je" bae kuma ce mata komae ba har aka kira sllhn Magrib snn ya mike ya shiga bathroom dinta yyi alwala ya ce ya tafi masallaci, Khaleel bae nufi masallacin da yasanxae hadu da dad dinsa ba, kuma ana idar da sllh ya dawo gida don ma kar su hadu bakin gate. Da kyar ya iya cin shinkafar da Ummi tayi masa ranan bayan ya dawo daga sllhn isha, Karfe takwas da kusan rabi Ashnaah ta tashi, Ummi ta kawo mata kunun da tayi mata, ta mike ta nufi bayi ta kuskure bakinta snn ta dawo ta dauki kunun tana sha, Karfe tara Khaleel ya shiga dakin rukayya yace ta duba masa falo ko dad na nn don xa su koma gida ne, ta dawo tace baya falo, komawa dakin umminsa yyi yace da ita xa su wuce gida, Ashnaah ta Mike ta dauki hijab din da Rukayya ta bata ta sa snn suka yi ma Ummi sae da safe, Ummi tayi masu Allah ya kiyaye suka fita daga dakin tana gaba yana biye da ita a baya, ido hudu Khaleel yyi da dad dinsa da sakkowansa falon knn yana cin fruit a kan centre table, Khaleel ya dauke kansa da sauri ya kasa ci gaba da tafiyar ya tsaya stairs din karshe, Ashnaah ta juya tana kallonsa, ita ma jikinta yyi sanyi, ta karasa falon a sanyaye ta isa inda dad din yake ta durkusa kasa ta gaishesa kanta a sunkuye, dago kai yyi yana kallonta, ya ajiye fork din hannunsa yana dan murmushi yace "lfya lau, kun xo lfya?" Ta dago Kai tace "lfya lau Abba," dad yace "to madallah, ashe kuna ciki nayi xaton kun tafi ne" ta girgixa kai tace "ba mu tafi ba" Dad yace "to yyi kyau, ya jikin naki?" Tace "da sauki Abba" yace "to Allah ya sauwake, ko xa ki ci kankanan ne in dibar maki" tayi murmushi tace "Aa nagode Abba" dad yace "A'a baria debar maki dae" murmushi ta kuma yi bata ce komae ba don sae taji kankanan ya bata sha'awa, dad ya dauki wani plate ya shiga deban mata kankanan snn ya sa mata toothpick ya mika mata, akunyace ta karba tare da yi masa gdya, yace "tashi ki koma kujera toh" kin tashi tayi ta shiga cin fruit din nn inda take, sae ta ji ina ma Abbanta ne hka, tunanin hka ya sa kwalla ya taru a idonta. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 103..... A hnkli Ashnaah ta daga kai a sanyaye tana kallon Khaleel da ke tsaye har lkcn, suna hada ido ya dauke kansa, Dad kam ci gaba yyi da shan fruit dinsa, Khaleel ya juya ya koma sama da ganinsa kasan jikinsa yyi sanyi, a hnkli tayi ta shan water melon din har ta kusa shanyewa bata ji ya isheta ba, dad yace "yaushe ku ka xo?" Ta daga kai tana kallonsa tace "daxu da yamma" yace "shine xa ku koma ynxu?" Shiru Ashnaah tayi bata ce komae ba, dad yace "ku bari sae da safe ku tafi" kai kawae ta gyada masa, ya dauki wayarsa ya kira driver yace ya shigo falo ya samesa, ko minti biyar ba ayi ba drivern ya shigo dad ya ciro dubu biyu ya mika masa yace "kankana masu kyau xa ka siyo mata" kunya ya kama Ashnaah don ko kadan bata lura da har ta shanye kankanan gabanta gaba daya ba, da sauri tace "A'a Abba ni na koshi" Dad yace "bari dae ya karo maki ki kara" bata kuma cewa komae ba, dad ya canxa tasha xuwa news ya maida hnklinsa. Bayan minti sha biyu drivern ya dawo rike da ledan water melon, ya ajiye ma Dad kan center table, ya mika masa canjin dubu daya yace "na ga dayawa oga" dad yace "to rike canjin kai ma sae ka siya ka sha" gdya yyi ya fita daga falon, dad ya mike da kansa ya nufi kitchen ya dauko wuka da plate ya dawo ya dauki kankanan daya ya yanka snn yyi slicin dinsa kan plate din ya dauki toothpick ta saka ya mika ma Ashnaah da ke ta kallonsa, a kunyace ta ce "lahh Abba ni ya isheni fa" Dad yace "A'a ki dae kara" karba tayi tayi masa gdya kuma, har kusan Karfe goma da rabi Ashnaah na xaune falon da dad, ta dae ji ta fara jin bacci ta mike tana kallon dad tace "Abba bacci nake ji" yace "to tafi kiyi kwanciyar ki," ledan sauran kankanan ya mika mata yace "ga shi ki tafiya da sauran, Wanda aka yanka kuma ki saka a fridge" gdya tayi masa ta karba snn ta dauki plates din da tasha fruit din da nasa da wukan ta kai kitchen, tsaf ta wankesu ta ajiye snn ta fito ta kuma yi masa sae da safe ta nufi sama ina ma Abbanta ne hka da ta more rayuwa, dakin Ummi Ashnaah ta nufa, ta tarda Ummi xaune suna kallo da rukayya, Ummi tayi mata murmushi tace "sae ynxu" Ashnaah tayi murmushin ita ma, ta ajiye ledan hannunta xa ta xauna kasa Ummi tace ta dawo kan gado, ta xauna gefen gadon, Ummi tace "yana can dakinsa in kina jin bacci ki tafi ki kwanta kar ki takura kanki" Ashnaah ta sunkuyar da kanta tace "to ga fruit Abba ya siya min" Ummi tace "to kin gode" mikewa Ashnaah tayi ma Ummi sae da safe xata fita daga dakin Ummi tace "to kin bar fruit din" Ashnaah tace "A'a na sha da yawa Ummi, na koshi" Ummi tace "to dauka ki kai ma Khaleel" bbu musu Ashnaah ta dauki fruit din snn ta kuma yi mata sae da safe ta fita ta nufi dakin Khaleel, a hnkli ta tura kofar dakin ta same shi durkushe kusa da fridge dinsa, gabanta yyi mugun faduwa ganin abinda ke hannunsa yana dubawa, tasan baxae wuce expire date yake dubawa ba, yana ganin ta ya mayar da sauri ya fiddo ruwa, ta dauke kanta ta ajiye ledan hannunta ta nufi kan gado, ya bi ta da kallo yace "yhu re back wife" kai kawae ta gyada masa ta kwanta gefen gadon ta juya masa baya kmr bata son mgna rufe fridge din yyi ya dawo kusa da ita ya xauna yace "jikin ne wife?" Girgixa masa kai tayi da kyar tace "bacci xan yi" yace "OK wife, amma bari ki fara shan drugs dinki" girgixa masa kai tayi da sauri tace "amae xan yi" bata jira cewarsa ba ta juya masa baya, mikewa yyi ya dauko blanket ya rufa mata, ta lumshe ido kmr me bacci, gefen gadon ya xauna ta daya side din yana danna wayarsa, har kusan sha daya Ashnaah bata yi bacci ba amma bata bari ya gane ba, mikewa ta ga yyi yana kallonta, ta rufe idonta gaba daya kmr me baccin gske, fridge ta ga ya nufa ya bude ya fiddo kwalban daxu yana kallonsa rabon sa da shan giya tun ran da ya sha a birthday, ganinsa yasa yaji kmr ya shekara goma rabonsa da sha, Ashnaah taji kmr tayi masa mgna amma ta kasa sae taji hawayen takaici na sakko mata, budewa taga yyi ya koma bakin gado ya xauna ya kai bakinsa ya shiga sha, ko second talatin ba ayi da kai shi bakinsa ba ta ga ya cire da sauri, juyawa tayi tana kallonsa don yasan ma ba bacci take ba, ya ajiye kwalban hannunsa kasa gefensa ya rike kansa, mikewa taga yyi da hanxari ya nufi bathroom ta bi sa da kallo, amae ta ji ya shiga yi, ko motsawa daga inda take bata yi ba, amae ssae yyi a bayin, daga karshe ya fito da kyar bae bari sun hada ido ba ya nufi can gefen gado ya kwanta ba tare da ya kalli kwalban da ya ajiye kasa ba don ko ganinsa ma bae son yi, nn da nn bacci ya daukesa. Ashnaah tayi murmushi ta mike ta dauki kwalban taga har ya kusa rabi, bayi ta shiga da shi ta toshe hanci don ko warin bata son ji, ta tuttular da giyan snn ta dawo dakin ta bude fridge ta fita da sauran ma gaba daya duk sae da ta tuttulesu a bayi hancinta a toshe snn ta wanke bayin da kyar don duk tayi weak, wanka tayi da ruwan dumi ta fito da kwalaban ta ajiye su dakin tayi kwanciyarta da xanin jikinta, nn da nn bacci ya dauketa ita ma, can cikin dare ta farka ta dalilin aman da ta dinga ji, ta mike xaune da kyar ta jingina jikin gadon xuciyarta na tashi, juyawa tayi tana kallon Khaleel taga baccinsa yake, mikewa tayi ganin aman na neman taho mata ta nufi bathroom da sauri, ta durkushe ta shiga kwararo aman, hkn ya farkar da Khaleel ya mike xaune da kyar ya rike kansa da ke juya masa. 104..... Mikewa yyi jikinsa a mace ganin har lkcn aman bae tsaya mata ba ya nufi bathroom din, dukawa yyi ya dafata ta turasa da sauri alamar ya kyaleta, komawa gefe yyi yana kallonta har ta gama ta mike ta wanke bakinta da mouth freshner ta fice ta bar masa aman a gurin. Gyara gurin ya shiga yi har ya gama snn ya hada ruwan wanka ko xae ji karfi a jikinsa, bakinsa ya soma wankewa snn yyi wanka ya fito daure da towel a waist dinsa, xaune ya sameta ta jingina jikin gado, suna hada ido ta dauke kanta da sauri don tun da suke bae taba fitowa hka daga wanka gabanta ba, kwanciya tayi ta shige cikin bargo ta rufe har kanta, ya gama sa sleepn robe dinsa yana kallon empty kwalaban da ta ajiye masa gefen fridge, dauke kai yyi da sauri don ko ganinsu bae son yi, agogo ya kalla yaga biyu saura, ya kashe wutan dakin ya kwanta yana kallonta, a hnkli ya birgina inda take ya cire bargon jikinta gaba daya, ta shiga turasa alamar ya rabu da ita, ya rungumeta a hnkli yace "Haba bbyna, am so srry plss" kuka ta sakar masa ya shiga lallashinta ta gaji don kanta tayi shiru, a sanyaye yace "wllh bana kara shan any Alcoholic drink wife, kin ma ga ya fitar min a kai ynxu, da na sha xan yi amae" shiru tayi bata ce masa komae ba, shi ma bae kuma cewa komae ba duk jikinsa yyi sanyi, a hnkli ta xame jikinta daga nashi ta juya masa baya. Washegari karfe goma suka gama shirin komawa gida, falo Ashnaah ta samu dad xaune ta durkusa ta gaishesa snn tace xa su tafi, dad yace "da wuri hka xa ku tafi" tayi murmushi bata ce komae ba, ya mike yace "to ina xuwa" sama ya nufa dae dae stairs suka hadu da Khaleel da ke sakkowa, Khaleel bae bari sun hada ido ba ya basa hanya da sauri, a sanyaye ya karasa sakkowa downstairs yana kallon Ashnaah yace "mu tafi" tace "Abba yace in jira shi" bae ce mata komae ba ya fita falon don yasan ko ya tsaya yi masa sallama ma ba tanka sa xae yi ba tunda bae amsa gaisuwarsa daxu ba, Dad ya sakko rike da kudi ya mika ma Ashnaah yace "to gashi ki siya duk abinda kike so" kasa kin amsa tayi ta karba a kunyace tayi masa gdya ta mike yyi mata Allah ya kiyaye hanya snn ta fita don sun yi sallama da Ummi, xaune ta tarda Khaleel cikin mota yana jiranta, tana shiga motar ya tada mai gadi ya bude masa gate ya fita. Karfe sha daya saura suka isa gida, Khaleel ya juya yana kallon Ashnaah yace "ki shiga ciki wife, xan je siyo maki magunguna kafin su kare daga nn sae in siyo abinci, me kike son ci?" Ashnaah ta girgixa masa kai tace "ba komae, xan sha kunun da Ummi tayi min" kudin hannunta ta mika masa tace "ga shi Abba ya bani" yyi murmushi yace "to kin gode wife" tace "to ka karba mana" ya girgixa kai yace "ae ke ya ba ma wife ki rike kayan ki kawae" bata rae tayi har lkcn tana mika masa, yyi murmushi yace "to ki shiga sae na dawo ki ban" ba musu ta bude motar ta fita ya bi ta da kallo har ta shiga gidan, snn ya juya ya fice da motar, kwanciya Ashnaah tayi kan kujera a falo, wayarta taji yana vibrate ta bude jakar ta ciro da sauri ta ga Ashfah ce ke kiranta, daga kiran tayi Ashfah tace "sister ba ki turo address din ba kuma, ya jikin?" Ashnaah tace "lah gashi ban tambayesa ba kuma baya nn, Bari in tambayi mai gadi," da sauri ta fita ta tambayi mai gadi address din layin ya bata snn ta gaya ma yar uwartata, Ashfah tace to ga ta nn xuwa. Cikin minti ashirin Ashfah ta iso gidan, Ashnaah ta ji ddin ganinta ssae ta rungumeta tana tambayarta momynta fa, Ashfah ta ajiye ledan abincin hannunta tace "ta ce a gaishe ki" a sanyaye Ashnaah tace "Abba ya dawo?" Girgixa kai Ashfah tayi, Ashnaah tace "to inna fa" Ashfah tace "tana nn" shiru Ashnaah tayi bata ce komae ba, can ta mike tana kallon yar uwartata tace "mu tafi sama" mikewa Ashfah tayi ta bi bayanta ta kai ta dakin da take. Hira suka dinga yi har kusan karfe daya suka yi sllh, Ashnaah da kasala da tashin xuciya ya isheta tace ma yar uwarta bari ta dan kwanta don ta gaji, tana kwanciya nn da nn bacci ya dauketa. Ashfah bata xauna ba ta shiga gyara ko ina na gidan, tana kitchen tana wanke dan kwanukan da ta gani Khaleel da Najeeb suka shigo gidan, kin fitowa tayi daga kitchen din har ya suka shigo falon da mmki Khaleel ke kallon ko ina na falon, bbu abinda ke tashi sae kamshi Mae ddi, ya kalli kofar kitchen jin karan ruwa ya nufi kitchen din da sauri, daga bakin kofa ya tsaya yana kallonta da mmki ganin ynda tayi kwalliya, ko kadan bae lura ba Ashnaah ba ce don mugun kamar da suke, Ashfah taki juyowa jin bae ce komae ba ta ci gaba da wanke wankenta, karasowa cikin kitchen din yyi yana murmushi yace "waww wife duk ke kika yi wnn aikin," da sauri Ashfah ta juya ganin ya nufota xae rungumeta tace "ba ita bace" cak ya tsaya yana kallonta, ta dauke kanta tana ci gaba da dauraye plates din hannunta tace "ina yini" Khaleel ya koma baya da sauri ya fara kame kame "ohh srry sister, lfya lau, sannu da aiki, yaushe kika xo" ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 105..... Ba tare da Ashfah ta juyo ba tace "Yauwa ngd" juyawa Khaleel yyi ya fita daga kitchen din da sauri ya koma falo, xaune ya tarda Najeeb ya kunna Tv yana canxa tasha hnkli kwance uwa falonsa, Najeeb ya daga kai yana kallonsa yace "kace jikin Madam yyi kyau knn tun da har ta fara aiki" kai kawae Khaleel ya gyada masa ya dauki ledan da ya shigo da ya nufi sama, Ashnaah ta fito daga bathroom knn ya shigo dakin, da ganinta kasan amae tayi, bata ko kallesa ba tayi kwanciyarta kan gado ya karaso ya xauna gefenta a hnkli yace "sannu wife" bata tanka sa ba sae ma juya masa baya da tayi, yace "ashe twin sis ta xo, tot ke ce a kitchen sae ta ce min ba ke bace" nn ma dae Ashnaah bata ce masa komae ba, shiru yyi bae kuma cewa komae ba, ta juya ta hade rae tana kallonsa tace "daga ce min ynxun nn xaka dawo shine xa kayi tafiyarka ka barni ni kadae a gida koh" ta karashe mgnr kmr xata yi kuka, Khaleel yace "ohhw am srry bbyna, Najeeb ne ya bata min lkci, but ae twin sis ta xo ta taya min ke xama toh" harara ta galla masa tace "ba ynxun nn ta shigo ba" yyi murmushi ya jawota jikinsa ya lumshe ido a hnkli yace "am so srry wife" lamo tayi bata ce komae ba. Ashfah na gama gyara kitchen din ta fito falo da nufin xuwa ta ce ma yar uwarta xata tafi, kallo daya tayi ma Najeeb da ke xaune falon ta dauke kai lkci daya ta ganesa, yana kallonta yace "ya jikin Fateema" bbu yabo bbu fallasa Ashfah tace "tana sama" bata jira ta kuma jin me xae ce ba ta nufi saman da sauri, Najeeb ya bi ta da kallo da mmki ya mike tsaye da sauri yace "wait! wait" amma tuni ta haura sama, kwankwasa kofar dakin tayi tare da yin sallama, Khaleel ya mike tsaye tare da amsa mata sallaman, Ashnaah tace "ki shigo mana sister" Ashfah ta turo kofan ta shigo tace "sister bbu wani abun da xa ayi maki koh? Xan tafi ne" Ashnaah ta hade rae kmr me shirin kuka tace "xa ki tafi fa kika ce Ashfah, yaushe kika xo" Ashfah tace "kin ga fa ina da lecture xuwa anjima" Ashnaah tace "ashe dama ba kwana xa ki min ba" Ashfah ta xaro ido tace "kwana kuma, ki bari nxt tym sis, ina da class yau" Khaleel yace "Haba sister ki kwana mana sae ki tafi gobe mana" Ashfah ta sunkuyar da kai tace "ka ga fa ba muyi da momy xan kwana ba wllh" Ashnaah tace "dan ara min wayar ka in kirata ni in gaya mata" Khaleel ya mika mata ta karba ta kira momynsu, momy na dagawa ta marairaice kmr xata yi kuka tace "Momy don Allah ki ce Ashfah ta kwana gobe sae ta tafi kin ga wae fa ynxu xata wuce" momy tace "Kinga Abbanku bae san ta fita ba kuma gobe xae dawo ki bari next tym kin ji" Ashnaah ta fashe da kuka tace "momy ba dawowa xata kuma yi ba fa nasani" Momy ta dan yi shiru snn tace "toh shknn amma gobe da sassafe ta taho kar ya dawo ya ga bata nn" Ashnaah tayi murmushin jin ddi tana share hawayenta tace "to momy ngdd" ta katse wayar ta juya tana hararan Ashfah ta ja tsaki ta mike ta fice daga dakin don xuwa ta dauko cup din da xata Debi kunu ta sha a kitchen, Khaleel yyi murmushi yana kallon Ashfah da mood dinta ya canxa lkci daya, yace "kiyi hkuri sister, yau da gobe ae duk daya ne koh" murmushi ta kirkira bata ce komae ba, kasa ci gaba da kallonta yyi don sae yake ganinta kmr Ashnaah don kmrsu tayi yawa, juyawa yyi da sauri kmr wnda ya tuna abu ya dauki hijab din Ashnaah ya bi ta da shi yana kiranta, Ashnaah da har ta kai stairs ta juya tana kallonsa ya mika mata yace "Najeeb na falo" karba tayi ta sa ta fita, tsaye ta tarda Najeeb har lkcn ya kasa xama idonsa a kan stairs, yana ganinta ya nufe ta da sauri yace "pls fateema kice twin sistern ki ta saurareni taki saurarata" Ashnaah tayi dariya tace "wae Ashfah, ae bata kula samari nn da ka ganta" Najeeb ya marairaice mata yace "Haba fateema kar muyi hka da ke mana, help me plss" Ashnaah tace "wllh da gske nake Ashfah bata kula saurayi," da mmki Najeeb yace "to sbda me?" Ashnaah tace "sbda Abbanmu ya hana, karatu ya fi so" Najeeb ya kasa daina mata kallon mmki yace "to ke ya aka yi har kika kula Khaleel ku ka yi aure, ko ita kadae ya sa ma dokar bn da ke?" Ashnaah tayi shiru tana kallonsa lkci daya jikinta yyi sanyi hawaye ya shiga taruwa idonta a xuciyarta tace "sbda bna jin mgnrsa ni" bude baki tayi xata gaya masa abinda ke ranta suka ji muryar Khaleel a bayansu, "enuf of those silly questns Najeeb" juyawa Ashnaah tayi ta nufi kitchen da sauri, Khaleel ya karaso kusa da Najeeb yace "wnn wace irin tambaya ce kke yi Najeeb" Najeeb da ganin Ashfah ya sa ya rude kwata kwata ya mance abubuwan da ke kasa ya fara kame kame, tsaki Khaleel yyi ya juya ya nufi kitchen, kuka ya tarar Ashnaah ke yi, ya karasa kusa da ita a sanyaye ya rungumeta ta kuma fashewa da wani Sabon kukan, sae da ya tabbatar tayi shiru snn ya barta ta fita daga kitchen din shima ya fito, Najeeb ya nufo sa da sauri yace "am so srry frnd wllh hnklina ya gushe ne, I get I wasn't supposed to bring up dis issue" Khaleel yace "its OK" Najeeb ya dan yi shiru snn yace "which help wil yhu render me in here plss Khaleel, I am blindly in love, wllh tsakanina da Allah nake son yar uwar matarka kuma da aure" Khaleel ya dan yi murmushi don tun da yake da Najeeb bae taba jin yace yana son mace da aure ba, yana shafa kansa yace "ni kuma a su wa a ynxu? Ita yarinyar xan ma mgna ko iyayenta da aka goga min kashin kaxa a gun su xan je in sa ma, ko kuma iyayena da ke fushi da ni har yau akan abinda bn aikata ba xan tura su yi ma iyayenta mgna cewar abokina na son yar uwar matata? Tell me hw dis is goin to be frnd" shiru Najeeb yyi yana kallon Khaleel lkci daya jikinsa yyi sanyi a xuciyarsa yace "but I am d cause of all dis," ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 106..... Juyawa Khaleel yyi ya bar sa wajen a tsaye ya koma kan kujera ya xauna, Najeeb ya runtse ido ya bude yana girgixa kai lkci daya ya share gumin da ke karyo masa ya dawo gefen Khaleel yana kallonsa boldly yace "wat if I claim being the one dat wrote dat divorce content?" Khaleel ya dago ido yana kallonsa, can yyi tsaki ya girgixa kai hade da tabe baki yace "go ahead mana, if yhu think dat will make yhu get her, u will only end up ruining matters, dat is addin salt to injury" Khaleel yyi murmushin da bae yi niyya ba yana kallon abokin nasa, lallai ya yrda Najeeb ya rikice kan Ashfah, Najeeb ya fuxa iska yace "it sound meaningless nd annoying ryt?" Mikewa Khaleel yyi yace "ka ga ka tafi gida ka bar min hauka a nn don Allah, in ka dawo nml koh xuwa anjima da daddare sae ka dawo let get a soln" Khaleel na kai wa nn ya dauki wayarsa ya nufi sama, Najeeb ya bi sa da kallo jikinsa yyi sanyi ssae, ya dafe kansa, yes! yasan no matter wat Khaleel baxae taba yrda shi ya rubuta takardan da ya tarwatse farin cikinsa ba ko jikinsa xae xama kunnuwa ne gaba daya, but hw is he goin to proof dat to him. Karfe takwas da rabi na dare Najeeb ya dawo gidan, Khaleel na kwance falo kan doguwar kujera yana kallon kwallo, yana ganinsa ya mike xaune, Najeeb ya karaso ya xauna yana kallonsa, Khaleel yace "kae da nace ana magrib ka xo malam, to gashi har sun yi bacci har fa nayi mata mgna daxu ta amince xata saurareka" Najeeb kwalalo ido yace "don Allah Khaleel, wllh daga clinic nake shi yasa bn xo da wuri ba, plss ka tashe ta mana" Khaleel yace "A'a ka dae xo gobe da safe xae fi" Najeeb yyi shiru bae ce komae ba, ba don ransa ya so ba ya mike yyi masa sallama ya fice, Khaleel ya bi sa da kallo har ya fita snn yyi dariya. Mikewa Khaleel yyi ya nufi sama yyi sallama ya shiga dakin da su Ashnaah su ke, Ashfah ce xaune kan darduma tana shafa'i da wutr, Ashnaah kuma tana bayi tana wanka, Khaleel ya rasa gane Ashnaah ce xaune kan darduman ko ba ita ba don hijab din Ashnaahr ce, ya dae yi assure din kansa ita ce, tsaye yyi bakin kofa yana jiran ta idar, dae dae nn Ashnaah ta fito daga wanka daure da towel, kallo daya yyi mata ya juya da sauri tare da cewa "oh srry sister" ya fice daga dakin, Ashnaah ta fashe da dariya har da kyakyatawa, Ashfah na idar da sllh tace "wae ba kin fi ni tsayi ba da haske" Ashnaah dake dariya har lkcn tace "gane min hanya, ko da yake mu ryt frm tym ba a iya banbance mu" Hijab Ashnaah ta sa tace ma yar uwarta tana xuwa snn ta fita, falo ta samesa xaune, ta kuma fashewa da dariya, ya mike yana kallonta da mmki, ta karaso tace "daga ynxu idan kana son sanin wacece fateema tsayin mu kawae xaka kalla," Khaleel ya sauke ajiyar xuciya ya jawota jikinsa yace "OK wife" xaunawa yyi kan kujera ya xaunar da ita kan kafarsa ta shiga kkrin mikewa da sauri ya rungumeta yace "kin ga kin dan fara samun sauki ynxu ko wife, bbyn nn nawa na son ki dayawa baya son wahalar da ke, just a month nd two wk fa yhu re gettin beta," Ashnaah ta galla masa harara tace "ko ba better ba, don kawae ina daurewa koh," kmr xata masa kuka ta karashe mgnr, Khaleel ya shiga kkrin cire hijab din jikinta a hnkli yace "to yi hkuri bbyna yhu re nt gettin beta" ta xaro ido ta rike da sauri tace "tawul kadae ne fa jikina" sake mata hijab din yyi ya shiga dagawa daga kasa a hnkli yana kallon santala santalan kafafuwanta, ya lumshe ido ya daura lips dinsa kan wuyanta murya can kasa kmr me rada yace "wife ki dan tausaya min yau mana, I i need yhu badly" Ashnaah ta hade rae ta fara kkrin tashi daga kafarsa ya rikota da sauri a hnkli yace "to kiyi hkuri wife, I won't again na bari" Karfe sha daya Ashfah ta ishe Ashnaah ta fi gun mijinta ta bar ta ta fara jin bacci, da kyar Ashnaah ta fita daga dakin ba dan ta so ba da sunan xata dawo idan tayi masa sae da safe. Dakin da tasan xata samesa ta shiga, kwance ta samesa yyi rub da ciki kan gado idonsa lumshe kmr me bacci ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 107..... Ashnaah ta karaso gefensa ta xauna tana kallonsa tace "re yhu sleepn" a hnkli ya bude manyan idonsa da suka sauya kala yana kallonta, ta mike tace "came to say gudnt" shiru yyi bae ce komae ba har lkcn idonsa na kanta, hade rae tayi ganin hka ta juya xata bar dakin ya mike xaune ya rikota da sauri ya dawo da ita ya xaunar gefensa, cikin wata kasalalliyar murya yace "am srry wife, me kika ce?" Kmr xata yi kuka tace "ba ka ma ji abinda nace ba koh" lumshe ido yyi ya rungumota a hnkli yace "wllh bn ji ba bby" shiru tayi bata ce komae ba kanta na kirjinsa, sun kusa minti goma a hka can dae ta dago tana kallon agogo ta ga sha daya ya kusa, ta shiga kkrin mikewa tace "xan tafi in kwanta sae da safe" kin saketa yyi, tace "don Allah ka kyaleni in je in kwanta" da kyar ya iya bude baki yace "baki tausayina ko wife?" Ta xaro ido xata yi mgna ya saka bakinsa cikin nata, ssae ta tsorata kmr ranan ya fara kiss dinta, ta fara neman kwace kanta amma ta kasa, hkn yasa ta sakar masa kuka jikinta na bari tana cewa ya bata so, Khaleel bae sarara mata ba duk da ynda ya ga ta rude daren nn har sae da ya kai ga cimma burinsa, bbu abinda take sae aikin kuka tana neman tashi ta bar masa dakin amma ya ki saketa, wani mugun haushinsa kawae take ji a lkcn duk da ta dan sha wahala amma ba kmr na farko ba, bbu irin lallashin da bae mata ba amma kamar 'da da tunxurata yake, ta gaji da kukan wajen Karfe daya bacci ya dauketa, can wajen Karfe uku ta farka ta Mike xaune da kyar ta dalilin xaxxabi da ke jikinta ga wani tashin xuciya da ta ke ji, kkrin sauka daga kan gadon ta shiga yi ya rikota da sauri ta fixge hannunta da karfi ta sauka, gabanta ya shiga faduwa tana tsoron kadda ta kasa tafiya yau ma, amma sae ta ji bata ji xafi ba, ta fice daga dakin da sauri, kasa shiga dakinta tayi ta nufi downstairs don ta ga akwae bayi, nn tayi wankan ta ta fito ta sa hijab xata koma dakinta, xaune ta gansa a falon, ta kauda kai da sauri ta nufi sama ya mike ya bi ta, kuka ta saki ta ki ci gaba da tafiyan, tsayawa yyi inda yake, cikin kuka tace "ni wllh ka kyaleni bana so" shiru yyi yana kallonta, a hnkli yace "kiyi hkuri wife, am srry" juyawa tayi ta haura sama da sauri, tana shiga dakin ta kwanta gefen yar uwarta nn da nn bacci ya dauketa. Washegari da safe Ashfah ta gama shirin tafiya wae tana da lecture, don takaici Ashnaah da ke kwance ga xaxxabin da ya sa ta gaba ga ciwon mara bata ko kalleta ba bare ta tanka mata, Ashfah ta karaso gefen gadon tace "kin ji sister, xan tafi" ba tare da Ashnaah ta kalleta ba tace "Allah ya tsare" Ashfah ta mike tace "Ameen, Allah ya kara lfya sae mun yi waya" Ashnaah bata tanka ta ba har ta fice, Ashfah tayi murmushi kawae ta sauka downstairs abun ta, falo ta samu Khaleel, ta karaso cikin falon tace "sae anjima ni xan tafi" Khaleel ya daga kai yana kallonta yace "da safe hka sister, baki yi breakfast ba ae" Ashfah tace "bana breakfast da safe sae eleven, ina da lecture ne" Khaleel ya mike yace "OK, bari in dauko makulli in ajiye ki" tace "A'a wlh ka bar shi xan samu napep idan na fita" bae saurareta ba ya nufi sama ya dauko makullin motarsa ya shiga bedroom da Ashnaah take, xaune ya sameta tsakiyar gado ta hade kai da gwiwa tana kuka, ya karaso kusa da ita yana kallonta bata jira me xae ce ba ta mike ta shige bayi ta kulle kofar, ya dan yi murmushi ya juya ya fita daga dakin, a hanya yake ce ma Ashfah ta bar Ashnaah tana ta kuka, Ashfah tayi murmushi tace "wae baxan tafi ba ga shi yau Abbanmu xae dawo, kuma bae san na tafi ko ina ba" Khaleel yace "gskya ne" har kofar gidansu ya ajiye ta ya bata dubu biyar tare da cewa ta gaida masa momy ta karba da kyar snn ta shiga gida yyi reverse ya bar anguwar, a tare suka yi parkin da Najeeb a kofar gida, Khaleel ya rike kai yana dariya har Najeeb ya fito daga motarsa snn shi ma ya fito, Najeeb yace "Allah ya sa sun tashi" Khaleel ya fashe da dariya yace "ynzun nn na mayar da ita gida, ko karyawa ta ki yi wae tana da lecture, lkci daya mood din Najeeb ya canxa yace "ya xa ka min hka Khaleel?" Khaleel yace "its nt my fault frnd" juyawa Najeeb yyi ya shige motarsa ya fixgeta a guje ya bar anguwar Khaleel ya bi sa da kallo yana murmushi. Washegari Asabar ba tare da Najeeb ya Bari Khaleel ya sa ni ba ya lallaba abokanan dad dinsa shi ma ya bisu xuwa can gidansu Ashnaah don ganin Abbanta, Abba na gida a lkcn, as usual da fara'arsa ya tare su snn suka gabatar masa da abinda ya kawo su kan cewa sun xo neman auren Ashfah, Abba ya dan yi shiru snn yana kallon Najeeb yace "ita ta ce ka turo koh?" Najeeb ya girgixa kai da sauri yacec"A'a Dad, hasalima ni bata taba kulani ba wllh shi yasa na ce bari in xo neman ixini a gida" Abokanan dad din nasa suka tsaya kallonsa da mmki don ba hka ya fadi masu ba, Ca yyi yarinyar tace ya turo manyansa in ji babanta, Abba ya dan yi murmushi yace "gskya ne" maida dubansa yyi ga bakin nasa yace "to xancen gskya 'ya ta karatu take ynxu, kuma sae ta gama xan bada aurenta kuyi hkuri dob Allah, kae in kaga kana sonta xaka iya jiran ta gama, saura mata shekara uku idan Allah ya yrda" mikewa abokan dad din Najeeb suka yi kowa ransa a bace, bbu wani kwakkwaran sallama suka fice daga falon, Najeeb kam kasa tashi yyi, ya marairaice ma Abban yace "wllh dad xan bari tayi karatunta baxan hanata ba" Abba yace "to ni bnyi niyar aurar da ita ynxu ba sae nn da shekara uku," mikewa Najeeb yyi jiki ba kwari yyi masa sallama ya fita daga falon. 108...... Dayz went by followed by month, wasa wasa yau cikin Ashnaah ya cika wata shidda da sati biyu cif ynxu kam bbu wani laulayi sae nauyin da tayi, tayi garau abunta cikinta ya fito ssae but bata da kwanciyar hnkli kullum cikin tunani da xubda hawaye take, hkn yasa bata kumari, bbu abinda ke sa Khaleel farin ciki sae idan ya tuna cikin yan biyunsa Ashnaah ke dauke da, sae dae har lkcn bbu wani improvement daga parent dinsu maxa gaba daya barin ma Ashnaah, duk da dad din Khaleel baya nuna mata komae yana mata kmr ynda xae yi ma Rukayya kuma yana tausayinta, Khaleel kam baya samun fuskarsa, amma duk da hka bae hanasa shigowa gidansa ba, har lkcn gidan Al-ameen suke xaune, lkci lkci Al-ameen din ya kan kawo masu xiyara da Maryam, ko mgnr neman aiki Khaleel baya yi duk da ynda frnds dinsa na arxiki suka damu ko wannensu na kkrin ganin yyi masa hanyar samun aiki amma Khaleel bae damu ba don har lkcn kwalinsa na gun dad dinsa, lkci lkci Najeeb kan kawo masu ziyara kuma yana taimakon abokin nasa ssae da foodstuffs, kuma yawanci duk shi ke siyo masu lafiyayyun kayan babies masu tsada, tun Khaleel na nuna masa baya so har ya gaji ya daina ya kyalesa kawae. Yau Sunday Ashnaah na kwance gefen Khaleel dake kallon football, jin tayi lamo jikinsa ya sa ya juya yana kallonta yace "ya dae wife" tayi shiru bata ce komae ba, hkn yasa ya ajiye remote din hannunsa ya dagota da damuwa don kusan ko da wani lkci bata da aikin yi sae tunane tunane yasan ta fara knn tunda tun da ta tashi bata yi ba, ya rungumeta a hnkli ya lumshe ido yace "wat again wife" ta kwantar da kanta kan kirjinsa a sanyaye hawaye na bin kuncinta tace "doctor ka kai ni in gaida Abbana yau," shiru Khaleel yyi bae ce komae ba, a hnkli tace "ka ji?" A sanyaye yace "toh ki shirya mu je wife" Karfe sha daya da rabi Ashnaah ta gama shirinta ta sa hijab dinta har kasa ta sakko downstairs ta samesa ta ce ta gama. Makullin motarsa kawae ya dauka don shi ma ya shirya suka fita daga gidan, sae kallon ynda take sa hannu cikin hijab dinta tana kare cikin jikinta take wae kunya, don Ashnaah akwae kunya ba kadan ba, dariya ma take basa duk lkcn da ya ga tana hka, barin idan sun je gidansu, sae da suka kama hanya snn ya juya yana kallonta ya ga duk tayi sanyi, lkci daya ya mayar da dubansa ga titi, a hnkli yace "me xa mu siya ma Abba wife?" Ta girgixa kai hawaye ya shiga xarya a kuncinta tace "bbu komae, gaishesa kawae nake son xuwa yi" shiru yyi bae ce komae ba, can yace "to momy fa?" Nn ma ta girgixa masa kai tace "A'a ka bar shi kawae" bae kuma ce mata komae ba har suka isa kofar gidansu wajajen Karfe sha biyu na rana yyi parkin yana kallonta, bude motar yyi ya fito ya xagaya ya bude mata ya taimaka mata ta fito. Hawaye ta shiga yi a sanyaye ta nufi gate dinsu yana biye da ita a baya. Nasan ba lallai ne ku iya gama karanta wnn ba har sae da rana tsabar yawan shi. Amma idan kun gama sae ku sanar da in ci gaba don ban san kanku ya dau xafi. Gud Mrnin Anties nd Momies. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 109.... A hankali Ashnaah ta murda kofar shiga falonsu duk da ta ga motar Abbanta a parkin space din gidan amma ta dake, a rufe taji kofar falon, hkn yasa ta dan yi jim snn ta danna bell jiki ba kwari ta dan koma baya, Khaleel kam kasa karaso balconyn yyi ya tsaya daga kasa, ba a dau lkci ba aka bude kofar falon, Ashnaah da gabanta yyi mugun faduwa tayi baya da sauri, Ashfah ce ta bude kofar, kasa cewa komae Ashfah tayi sae kallonsu take da mmki, Ashnaah tayi karfin halin yin murmushi tace "sister" Ashfah ta kasa amsawa ta dalilin tambayar da Abbansu dake xaune a falo ya jefo mata na cewa "waye?" Ta juya tana kallonsa ta kasa ba sa amsa, mikewa Abba yyi ya karaso bakin kofar yana ce ma Ashfah halan bakya ji na ne, kallo daya yyi ma Ashnaah ya juya ya bar gurin, Ba Ashnaahr ba har abinda ke cikinta na tabbata sae da suka tsorata, Ashfah ta sakar mata murmushi bayan Abba ya bar wajen tace "shigo mana sister" can ciki tayi mgnr kmr me gudun kadda Abbansu ya ji ta, Ashnaah ta juya tana kallon Khaleel snn ta shiga falon a sanyaye, Ashfah ta kalli Khaleel din shi ma tace "ka shigo mana" murmushi yyi mata duk da bae yi niyar shiga ba ya shigo da confident din xae yi toleratin duk wani rashin mutuncin da Abbansu xae yi masa, Ashnaah bata ga Abbanta a falo ba, hkn yasa ta nufi sama dakin momynta, momy ta mike da mugun mmki tana kallonta, kuka Ashnaah ta fashe da ta silale nn kasan dakin, momy ta karaso da sauri ta dagota tana tambayarta daga ina take kuma me ya faru, da kyar Ashnaah ta saida kukan ganin ynda hnklin momynta ya tashi, a sanyaye tace "daga gida nake momy" momy tace "mijin naki fa" Ashnaah ta sunkuyar da kai tace "tare muke, na xo gaida abba na ne ko baxae amsa min ba" tana fadin hka ta kuma fashewa da kuka, momy ta sauke ajiyar xuciya cike da tausayinta tace "to ya isa ki daina wnn kukan, in ma bae amsa ba kansa" Abba kam dakinsa ya koma ya dauki makullin mota ya sauko falo fuskar nn tasa a daure, Khaleel da ke xaune falon tun da ya kallesa sau daya bae bari sun sake hada ido ba, Abba ya karaso cikin falon ya kwashi wayoyinsa dake kan centre table, Khaleel ya sakko har kasa ya gaishesa, ba tare da ya kallesa ba ya amsa har da tambayarsa ya aiki snn ya fice daga falon gaba daya, fitar motarsa momy ta ji ta tabe baki, ta kalli Ashnaah da ke shirin binsa dakinsa tace "to gashi ya fice, kar ki damun kanki Allah ya ga nufin ki" Ashnaah ta gyada mata kai tana kkrin mayar da hawayen da ke neman xubo mata ta koma ta xauna, momy kuma ta sauka downstairs suka gaisa da Khaleel, ranar ce rana ta farko da ta fara ganinsa shi ma hka ranan ya fara ganinta, Ashfah ta kawo masa ruwa ta ajiye masa yace ya gode, ko minti sha biyar ba ayi da fitar abba ba ya kira momy, da kmr baxata daga ba sae kuma ta daga, bbu yabo bbu fallasa ya fara mgna "kina ji na koh, to wllh na kuskura na dawo gidana naga yarinyar nn duk abinda nayi mata ita ta siyar ma kanta, maxa maxa ta bar min gida in ma ke kika gayyato ta kar ran ku ya bace daga ke har ita" momy ta tabe baki ta ajiye wayar, ko kadan bata nuna ma Ashnaah Abbanta ne ya kira ba amma ta gane, ko minti biyar bata kara ba ta mike a sanyaye tace "xa mu tafi momy" momy ta bata addu'o'in da xata dinga yi ta mata gdya snn suka wuce. Har suka isa gida bata ce komae ba hka ma Khaleel, through out ranan rasa gane kanta yyi ga shi ta ki cin komae sae kwanciya. Yana dawowa daga mosque bayan sllhn isha ya xauna gefenta da damuwa yace "plss wife, ki daina daga min hnkli don Allah" a sanyaye ya karashe mgnr, Ashnaah ta mike xaune bata ce komai ba, ya dauko abincin da ya karbo mata a gida yace "ga abinci Ummi tace a kawo maki" ta kalli abincin snn ta mike da kyar tace "xan wanke baki" bayi ta nufa ya bi ta da kallo cike da tausayinta ko minti daya ba ayi da shiganta ba ta fasa wani ihu, ya mike da sauri yana tambayarta me ya faru a rude ya shiga bayin. Wnn kam nasan har gobe ba lallai ne wasu su gama karanta shi ba tsabar yawa, all the same in kun gama goben koh da rana ne ku sanar da ni in daura plss.. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 110..... A durkushe Khaleel ya sameta a bayin, ya karaso da sauri shi ma ya durkusa yace "me ya faru" cikin kuka tana yarfe hannu tace "faduwa nayi" da damuwa yace "faduwa kuma? Garin ya?" Kin basa amsa tayi sae kuka take, ya dagota yana kallonta yace "ta ya kika fadi?" Ta girgixa masa kai tace "ni ma bn sani ba" kama hannunta yyi suka fita daga bayin ya xaunar da ita gefen gado yace "ki gaya min ta ynda kika fadi mana wife? Kuma me ya fadar da ke?" Ta share hawayen fuskarta tace "bn sani ba na xubar da ruwa sae na xame" yace "to ina ke maki ciwo ynxu?" Ta kalli kafarta tace "kafata amma ya daina ynxu" ya dudduba mata kafar snn ya Mike ya dagota a hnkli suka koma bayin, ya taimaka mata ta wanke bakin snn suka fito ya xuba mata abincin ta karba ta fara ci a hnkli. Da daddare ya fita ya siyo mata magunguna ta sha ganin sae complain take masa kafarta na ciwo, tana gama sha bacci ya dauketa, shi ma ya gama abinda xae yi ya kwanta. Can cikin dare kukanta ya tashe shi, ya mike xaune yana kallonta yace "me ya faru kuma?" Sanin wani lkcn hka take sa shi gaba cikin dare tai ta yi masa kuka ba dalili, da kyar ta iya bude baki tace "Cikina ke man ciwo da mara" ya sakko daga kan gadon ya dawo inda take yace "ciki kuma?" Gyada masa kai kawae tayi, yace "ki gaya min plss wife, ta ya kika fadi?" Cikin kuka tace "ni bn sani ba, kawae na ga na fadi ne" Khaleel ya girgixa kai da damuwa ya dagota yana mata sannu, hka ta hanasu bacci daren ranan sae kuka take ita cikin ta na ciwo, da asuba yana idar da sllhn ya tafi hsptl da ita ko scan ne ayi mata tun da bae san ta ynda ta buge ba, Karfe sha biyu saura suka dawo gida da Najeeb, suna shigowa falo ta kwanta kan kujera nn da nn bacci ya dauketa, Khaleel ya ajiye ledan magungunan hannunsa kan table ya xauna ya jinginar da kansa jikin kujerar, Najeeb yace "she wil b alryt frnd in'sha Allah," Khaleel ya gyada masa kai kawae bae ce komae ba. Sae kusan Karfe biyu Ashnaah ta tashi, Khaleel da ke xaune har lkcn a falon ya dawo gefenta ya dagota yana kallonta yace "sannu wife, ya cikin ya daina?" Gyada masa kai tayi kawae, ya cire mata hijab din jikinta yace "gobe xa mu je a gyara kwanciyar bby koh?" Ta hade rae sae kuma ta fashe da kuka tace "ni dae bna so, irin na daxu xa ayi min" ya girgixa Kai yace "A'a wife wnn daban" mikewa yyi ya dagota yace "mu je sama ki sha tea" Sae da aka kusa sati biyu Ashnaah ta samu saukin ciwon cikin, ta dawo nml sae dae me, kwata kwata Khaleel ya kasa gane kanta shirunta ya fi na ko wani lkci, abinci sae yyi da gske da ita take ci, idan ya tambayeta abin da ke damunta sae tace Abbanta, hkn yakan sa yaji tausayinta ssae, kullum yyi sllh sae yyi mata addu'an Allah ya daidaita ta da mahaifinta ko hnklinta xae kwanta, kusan duk kwana biyu sae ya kira mata momynta sun gaisa hkn ya lura na sa ta farin ciki, duk lkcn da ya ga mood dinta da kyau ya kan kai ta can gidansu gun umminsa ta wuni, wani lkcn su dawo ranan ko kuma Washegari, ana hka har watan haihuwarta ya tsaya. Yau Sunday tana kwance idonta biyu sae dae tayi xurfi cikin tunanin da take Khaleel ya shigo dakin rike da abincin da ya je gida ya karbo mata, juyawa tayi tana kallonsa ya sakar mata murmushi ya dawo kusa da ita ya xauna ya dagota yace "sannu da kwanciya wife, nace ki dan dinga motsa jikin ki ba kya ji koh" shiru tayi bata ce masa komae ba ya tsura mata ido, tayi masa wani mugun kyau ga hasken da ta kara, wara masa manyan idonta tayi ganin ynda yake kallonta sae kuma ta sunkuyar da kanta tana murmushi, shi ma murmushin yyi ya rungumota a hnkli yace "I've a surprise for yhu wife" dago kai tayi tana kallonsa, ya fiddo wasu takardu a aljihunsa ya mika mata yana murmushi, ta karba ta shiga budewa, idonta ya sauka kan receipt da admission lettern ta da ta taba xubarwa da ddewa farkon fara remedial dinta, dago kai tayi da mmki tana kallonsa tace "ina ka ga wnn?" Yyi mata murmushi yace "ran da kika xubar da su ranan na tsince su?" Ta wara ido tana kallonsa, yyi yar dariya ya rungumeta ya lumshe ido yace "su nayi niyar baki ranan da kika mareni, I helped yhu pick them" hawaye ne ya cika idonta a hnkli tace "to ka yafe ni plss" dago kae yyi da sauri yana kallonta yace "kuka kuma? Haba bbyna ae dat day was the happiest day of my life wllh, baxan taba mance ranan ba wife, nd beside its nt ur fault its mine, I caused everything," Ashnaah ta kwanta kan kirjinsa a hnkli tace "ni dae ka yafe min duk abinda nayi maka tun daga farkon haduwar mu har xuwa yau" rungumeta yyi a sanyaye yace "ni ma ki yafe min wife" tayi murmushi hawaye na bin kuncinta shi ma sae ya samu kansa da xubda hawayen, a hnkli yace "kin san me yasa na kawo maki wife?" Ta girgixa Kai, yana shafa gashin kanta murya can kasa yace "today mark a year da haduwar mu, yau shekara daya da tsintar takardun nn da nayi" murmushi tayi yace "I love yhu" a hnkli tace "I love yhu more" Da daddaren ranan ta dame shi tana son ya kai ta gun momynta ta gaisheta, bae mata musu ba yace su shirya to su je. Karfe takwas da rabi suka isa kofar gidansu, sae a snn gabanta ya fara faduwa ta dae dake ta fito daga motar, Khaleel na kallonta a hnkli yace "amma Abba baya nn koh?" Ta girgixa kai tace "ni ma bn sani ba." Yace "to ki shiga xan jira ki a nn" ta gyada masa kai ta nufi gate dinsu 101...... A bude Ashnaah ta samu falonsu, ta tura a hnkli ta shiga, Abba na xaune yana kallon news kallo daya yyi mata ya dauke kai, gabanta ya fadi, ta dake ta karasa inda yake a sanyaye, duk da ynda cikinta yyi mata nauyi hkn bae hanata dukawa har kasa ta gaishesa ba, har ta cire ran amsawarsa sae kuma taji yace "lfya lau" rasa abun cewa tayi kanta a kasa, kmr a mafarki taji yace "ya jiki" ta dago kae da kyar tana kallonsa hawaye ya shiga bin kuncinta a hnkli tace "da sauki" jin bae kuma cewa komae ba yasa ta Mike da kyar ta juya ta nufi sama, momy tayi mmkin ganinta daren, ta kuma ji ddin ganinta, Ashnaah ta dde suna hira da momynta da Ashfah har kusan tara snn momy tace ta bar mijinta fa a waje, Ashnaah tace "ynxu xan tafi momy" momy tace "amma Abbanku baya falo koh?" Ashnaah ta dan yi shiru snn a hnkli tace "na gansa kuma na gaishesa ya amsa" sae kuma ta fara hawaye a sanyaye tace "kila ya yafe min momy, ke ma ki yafe min duk abinda nayi maki don Allah" kuka ne ya ci karfinta, hawaye ya shiga bin kuncin momy ta rungumeta tace "ni ba ki min komae ba Fateema, kuma na yafe maki duniya da lahira, Allah ya sauke ki lfya" Ashnaah ta gyada mata kai hawaye na ci gaba da bin kuncinta a sanyaye tace "Ameen momyna ngd, xan iya xuwa gaida inna don Allah" momy tace "tana katsina ae Fateema" mikewa Ashnaah tayi tana share hawayen fuskarta tace "to xan tafi momyna sae mun yi waya" Ashfah da ita ma ke hawayen ta mike don raka yar uwartata momy na biye da su a baya, falon Abba Ashnaah ta nufa ta duka kanta a kasa a hnkli tace "sae da safe Abba" Abba ya gyada mata kai yace "Allah ya tashe mu lfya" Ashfah na kallonsa a sanyaye tace "xan rakata waje Abba" kai kawae Abba ya gyada mata ta juya da sauri ta bi bayan yar uwar tata, har bakin mota ta rakata suka gaisa da Khaleel snn tayi masu sae sa safe Ashnaah ta daga mata hannu tana murmushi suka bar anguwar, Khaleel ya kalleta bayan sun hau kan titi yace "yhu seem Happy wife" Ashnaah ta dan yi murmushi a hnkli tace "Abbana ya amsa gaisuwana yau" Khaleel yyi murmushin jin ddi yace "Ma'sha Allah, am also happy for yhu wife" tana kallonsa tace "thank yhu, ka kai ni in gaida dad mana" ya dan yi shiru sae kuma a hnkli yace "toh wife" tayi murmushi tace "amma ko baxae amsa ka ba ka gaishesa plss" ta karashe mgnr a sanyaye, nn ma shiru yyi snn yace "toh wife" tara da minti talatin da biyar suka isa gidan, har falon dad Ummi ta kai ta bayan sun gaisa, dad ya rage volume din news din da yake kallo ganinsu yace "sannu da xuwa, daga ina ku ke hka da daren nn" Ashnaah ta xauna kasa tace "daga gida muke Abba" dad yace "Ma'sha Allah, yi xaman ki kan kujera toh" tayi murmushi tace "A'a nn ya isa Abba ina yini?" Ya amsa mata yana murmushi, dai dai nn Khaleel ya shigo falon kansa a kasa ya durkusa ya gaida dad dinsa, ba tare da ya kallesa ba ya amsa, Khaleel ya Mike ya fita daga dakin, sun dde xaune da dad dake ta kallon news, can tace "Abba xa mu koma," Dad yace "baxa ku kwana nn ba, ae dare yyi" tayi murmushi tace "A'a tafiya xa mu yi Abba" yace "to shknn," mikewa tayi xata fita ya saida ta, ya dauka wayarsa ya kira Ummi, ba a dau lkci ba ta shigo, yace "ki bata sako na" Ummi tace "toh" snn suka fita dakin da Ashnaah bayan tayi masa gdya duk da bata san menene ba, dakin Ummi suka shiga, Khaleel dake xaune yana danna wayarsa ya dago kai yana kallonsu, Ummi ta bude ward robe dinta ta shiga fiddo ledoji dauke da kayan bbies masu tsada, Ashnaah ta dan komawa baya kanta a kasa, kaya ne masu yawan gskya kuma yawancinsu duk na waje ne, sae da momy ta gama fiddo su gaba daya snn ta kalli Ashnaah da ta kasa dago kae ta kalleta tace "gashi dad dinku ya siya maki" hawaye ne ya shiga sakkowa idonta ta kasa kallon ummin, a hnkli tace "na gode Ummi," Ummi tayi murmushi tace "aa ki je can ki masa gdya ba ni na siya maki ba" Ashnaah ta juya a sanyaye ta fita daga dakin ta koma falon dad ta durkusa har kasa hawaye na ci gaba da bin kuncinta tace "mun gods Abba, Allah ya kara budi" yyi murmushi yace "bbu komae dota" kasa tashi tayi ta bar dakin, a sanyaye tace "Abba ka yafe mana kuma" Dad yace "tashi ki je, Allah yyi maku albarka" mikewa tayi da kyar ta fice daga dakin, har suka koma gida Ashnaah bata daina kukan da take ba. Washegari litinin Karfe sha daya Najeeb ya shigo da sallama, Ashnaah ce xaune kadae falon rike da hisnul Muslim tana dubawa, ita kadae tasan abinda take ji tun tashin ta ranan amma taki barin Khaleel ya gane, wani ciwon bala'i bayanta da kwankwasonta ke mata, ta dauki hijab dinta ta sa suka gaisa tana kirkiran murmushi yace "Khaleel baya nn ne" tace "yace min yana xuwa ynxun nn, ya je pharmacy" Najeeb ya shafa kansa yace "OK, yauwa dama ina son wata mgna da ke Fateema" Ashnaah ta maida hnklinta tace "ina jin ka toh" ya dan yi shiru sae kuma yace "dama I only want to ask for ur forgiveness fateema, I caused everything yhu nd ur husband are goin through" Ashnaah tayi shiru tana kallonsa da confusion, ya gyada mata kai yace "yes! I wrote dat divorce content, sae dae in baki manta ba ke kika taba bukatan hka" hawaye ne ya cika idonta, a hnkli yace "na gaya ma Khaleel bae yrda ba don a tunaninsa baxan taba masa hka ba, amma ni ne nn na rubuta, da fatan xa ki gaya masa ki kuma rokan min shi ya yafe min" Ashnaah ta gyada masa kai a sanyaye tace "its OK" yyi murmushi ya mike yace "I will b on my way, ki gaida min shi idan ya dawo" kasa amsawa tayi ta dalilin wani axababben ciwo da mararta ya shiga yi mata, lkci daya bayanta da kugunta suka dauka su ma, Najeeb ya lura da halin da ta shiga lkci daya ya ce "ya dae?" Kasa basa amsa tayi, ta shiga yarfe hannu don axaba, ya dawo kusa da ita lkci daya ya gane labour ne ya xo mata, Ashnaah ta kasa daurewa ta fashe masa da kuka, ganin bbu wani alternative yasa ya dagota kawae ya ja ta suka fita daga falon da sauri, ba karamin daurewa tayi ba har suka isa motarsa ya bude bck seat ya taimaka mata ta shiga ya tada motar ya nufi asibitin dad din Ameesha da ita da sauri ganin nn ne kadae baxa a bata masu lkci ba, bbu bata lkcin kuwa aka karbeta aka nufi labour ward da ita, Ashnaah kam bata san inda kanta yake ba a lkcn nn, amma bbu abinda ke fitowa bakinta sae salati, can kuma tace ita ina Abbanta. Najeeb ya fice daga ward din ya Ciro wayarsa a aljihu ya shiga kiran Khaleel yana dagawa yace "ka taho clinic Khaleel, na je gida na samu fateema na labour" a rude Khaleel yace "wani asibitin" Najeeb ya gaya masa, a fusace yace "don me xaka kai ta wnn asibitin, gsya baka kyauta min ba Najeeb" Najeeb ya katse kiran ya nufi inda Ashnaah take don ganin halin da take ciki. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 112..... Khaleel na shigowa clinic din ya nufi labour ward hnklinsa a tashe ba tare da ya bi ta kan nurses din dake reception ba, suka ci karo da Najeeb, Najeeb ya rikosa yace "kana da nmbr Dad dinta?" Khaleel ya fixge hannunsa xae ci gaba da tafiya Najeeb ya fixgosa a fusace yace "da'lla ka saurareni malam" Khaleel yace "me xa ayi da shi" Najeeb yace "dad din Ameesha yace I shud ask yhu, yhu knw! she's just giving headache in there sae Abbanta take kira, just cal him kadda ta ja ma kanta da babies din cikinta wani harm" Khaleel ya dafe kansa ya juya xae shiga room din Najeeb ya kuma rikosa yace "Cool down man, she's OK ka bani nmbr dad dinta kawae" khaleel ya girgixa kai da kyar yace "bani da shi, I dnt have" yana kai wa nn ya kuma juyawa da sauri Najeeb ya kuma rikesa yace "ka kwantar da hnklin ka frnd xata sauka lfya idan Allah ya yrda, ko nmbr mum dinta gare ka ka bani kawae, we will get to her dad through d mum" khaleel ya fiddo wayarsa a sanyaye ya shiga neman layin mum din Ashnaah, Najeeb ne ya karba wayar ya ja sa suka fita xuwa haraban asibitin, bin sa kawae khaleel yake ba don yasan yana yi ba, bugu biyu momy ta daga, Najeeb ya gaisheta snn yace "em momy abokin mijin fateema ne, dama da Abba muke son mgna don Allah" momy da lkci daya hnklinta ya tashi ta dake tace "lfya?" Najeeb yace "lfya lau, Fateemar ce dae ke nakuda, kuma ta dage tana son ganin abbanta, don Allah ki masa mgna momy kar wani abun ya sameta, kila idan ta gansa xa ta samu nutsuwa, har Allah ya sauketa lfya" momy da gaba daya hnklinta ya gama tashi tace "toh bari in gaya masa, wani asibitin ne don Allah" Najeeb ya gaya mata asibitin, momy ta katse wayar hawaye na bin kuncinta ta fito da sauri don xuwa gun mai gidan nata da ke falo, kasa ce mata komae Abba yyi yana kallonta can ya mike a hnkli ya dauki makullin motarsa yace "wani asibitin ne?" Momy ta gaya masa ya juya ya fice. Duk ynda khaleel ya so shiga labour ward ya ga Ashnaah kin barinsa dad din Ameesha yyi, wani doctor faruqh ya ja sa suka fita can haraban asibitin ya ajiye masa kujera yace "ka xauna nn plss kar ka kuma shigowa ko da reception ne, sae kace ba likita ba khaleel cool down plss Allah xae sauke matarka lfya kai ta mata addu'a kawae" Khaleel ya xauna ya dafe kansa dake sara masa bae ce komae ba, Likitan ya juya ya koma cikin asibitin, har Abban Ashnaah ya shigo asibitin Khaleel bae lura da shi ba, Abba na shiga reception Najeeb ya nufo sa da sauri yace "sannu da xuwa Abba, mu je ka ganta" bin sa kawae Abba ya shiga yi bae ce komae ba, dai dai bakin ward din suka hadu da dad din Ameesha ya fito da wani likita da ya tura ya kira masa Khaleel kawae ya xo ya sa hannu ayi mata cs don bae ga alamar xata iya haihuwa da kanta ba, yana kallon Abba yace "kai ne mahaifinta koh Alhaji?" Abba ya gyada masa kae kawae, dad din Ameesha ya koma cikin ward din ba a dau lkci ba ya fito yace "ka shiga ka ganta Alhaji," Abba ya tura kofan ya shiga Najeeb na biye da shi a baya, kasa karasawa ciki yyi yana kallon yar tasa, idonta rufe gam ta rike hannun Ameesha da ke ta tofa mata addu'a, bbu abinda ke fitowa bakinta sae salati in tayi tayi ta gaji sae kuma tace ina Abbanta ita a kira mata shi, nurses uku ne kanta da likita daya, Abba ya karaso ya dan duka kusa da ita yana kallonta yace "am here daughter," bude ido tayi da sauri lkci daya ta tsaida surutan da take ta shiga kkrin mikewa xaune ya dakatar da ita ya rike hannunta cikin nasa yace "kar ki damu fateema, yhu will b alryt in'sha Allah" ta kuma fashewa da kuka da kyar ta bude baki muryarta na rawa tace "don Allah don annabi ka yafe min Abbana" Abba ya girgixa mata kai a hnkli yace "na yafe maki da ddewa fateema, yhu will b alryt dota, kiyi ta addu'a" ta fashe da wani matsanancin kuka ta rike hannunsa gam muryarta na rawa tace "da gske Abbana" Kae kawae Abba ke iya gyada mata, ta saki salati tana girgixa ta dalilin wani axaba da take ji lkci daya ta shiga kkrin mikewa kuma, Abba ya mayar da ita shi ma ya shiga tofa mata addu'an, axaban da take ji bae sa ta rufe baki ba tace "Abba momyna fa ina take" Abba bae ce mata komae ba sae adduan da yake ta tofa mata yana rike da ita. Ba karamin wahala Ashnaah ta sha ba don har an fara shirin shiga da ita theatre ta sullubo santalelen danta ko minti daya ba ayi ba dan uwansa ya biyo sa, bbu abinda ke fitowa bakin ta sae salati tana rike da hannun Abbanta da ke kanta har lkcn idonta a runtse, a hnkli ta bude idanuwanta ta shiga kkrin bude baki da nufin yi ma abbanta mgna amma ta kasa, ya duka don jin me xata ce ya ga ta soma cika hannunsa daga nata a hnkli har ta sake gaba daya, lkci daya ya ga kmr komae na ta ya tsaya, a rude ya kamo hannunta yace "fateema" Ameesha da ke kallon duk abinda ya faru ta koma baya da sauri lkci daya ta juya masu baya ta runtse ido xuciyarta na bugawa, dad dinta ya taho da sauri yana kallon Ashnaah a sanyaye, Dr Faruqh ne yyi karfin halin dauko stethoscope ya dawo ya shiga duba ta, Najeeb ya ajiye yaron hannunsa ya karaso da sauri ganin ynda faruqh ya tsaya kmr gunki yana kallonta, fixge stethoscope din yyi ya shiga dubata, faruqh ya juya ya fice daga ward din kawae, Abba da gaba daya ya gama rudewa yace "plss ku gaya min wats wrong, wats wrong with my dota" Najeeb ya hade kansa da abun gado ya kasa dagowa. Infact duk Wanda yasan chapter din nn yyi masa sugar ya taho mu kwashi shoki, lol, Wanda kuma yasan bae masa sugar ba toh I assure him dogon suma tayi. Masu kkrin hacking fcbk accnt dina kuma su rufamin asiri su yi hkuri bata mutu ba ehe, Lol. I dedicate this page to Rukayya Usman Adam Allah bar min ke kawalli. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar113.....Najeeb ya mike da kyar idonsa ya kada yyi jajur ya juya xae fita daga dakin, Abba ya fixgosa hnkli tasheyace "na ce ku gaya min me ya sameta pls" hawayene suka sakko idon Najeeb yana kallon Abba, ya juya kawae ya fice daga ward din da sauri, Abba ya bi sa da kallo a sanyaye lkci daya ya xare glass din idonsa yana furta innalillahi wa inna ilaihi raji'un ya juya yana kallonta yana girgixa kai ya nufe ta da sauri ya rike a rikice yana cewa "No! No! It can't be, y fateema, plss kar kiyi mana hka" hawaye suka shiga xubo masa shi ma ya hade kai da abun gadon har lkcn yana rike da ita, dad din Ameesha ya xare glass din idonsa shi ma idonsa ya kada ssae ya karaso kusa da Abba ya dago sa yace "dats nt the right thing to do now Alhaji," a hnkli ya kara da cewa"pray for ur dota" Abba ya rikosa a rude yana girgixa kai yace "are yhu tryn to tell me she's no more" dad din Ameesha bae ce komae ba, Abba ya kuma hadekae da gado yana hawaye ssae, Dad ya juya yana kallon Ameesha da ke durkushe sae rusa kuka take kmr ranta xae fita, ya karaso kusa da ita ya dagota, cikin rawar murya tace "dad she's gone" rungumeta yyi a hnkli yace "yes dota, yhu only pray for her now," ta kuma fashewa da wani matsanancin kukan da yafi da muryarta ta rawa tace "Khaleel...." Dad dinta ya dago kanta yana rarrashinta, Najeeb na fita daga asibitin Khaleel da ke xaune har lkcn a haraban hsptl ya mike da sauri ya nufo sa, da damuwa kmr xae masa kuka yace "plss frnd ka gaya min halin da ake ciki, how's my wife" Najeeb da ke ta ci gaba da tafiyarsa ba tare da ya kallesa ba yace "da'alla malam ka rabu da ni, I've told yhu several times, she is OK" yana fadin hka ya fice daga gate gaba daya Khaleel ya bi sa da kallo, mancewa da warning din dad din Ameesha yyi ya nufi cikin asibitin da sauri, ko wacce nurse ya tambaya sae tace "she is OK dogon nakuda take" duk ya xama abun tausayi, ya ja gefe ya tsaya a reception din. Abba ya kusa minti goma kansa na kife kan gadon da Ashnaah ta ke har lkcn, Dad din Ameesha ya dago sa ya lulluba mata xanin gado yace "take heart Alhaji kar ka mance cewa kullum nafsin xa'ikatul maut, addu'a kawae xaka yi ma 'yar ka, mu ma idan ta mu ta xo Allah sa mu cika da imani" Abba da hawaye ya kasa tsaya masa bae ce komae ba ya ciro wayarsa da ke ring a aljihunsa, momy ce ke kiransa, ya mayar da wayar yana kallo. Ashnaah ya duka yana kallon Ashnaah hawaye ba sakko masa, a hnkli hawaye yace "Allah ya ji kan ki fateema ya yafe ma ki duk kurakuranki yyi maki rahama ya haskaka kabarin ki, ya raya abinda kika bari, na yafe maki duniya da lahira baki min komae ba fateema......" Kasa ci gaba yyi ta dalilin tokarewa da muryarsa yyi hawaye na ci gaba da sakko masa, dad din Ameesha ya dago sa yace "Ameen Alhaji, Allah yyi Mata rahama ya amshi shahadar ta" da kyar Abba yace "Ameen," snn ya ciro wayarsa jin momy na ta kiransa, ya fiddo handkerchief ya sharefuskarsa ya daga kiran, daga daya bangaren momy tace "ta haihu ne Alhaji, wllh hnklina ya kasa kwanciya tun daxu" Abba da wasu sabbin hawayen suka xubo masa ya dake yace "ehh ta haihu Alhmdllh" cike da murna momy tace "Alhmdllh, me aka samu?" Abba ya juya yana kallon yaran da ke kwance nurses sun gama gyara su a hnkli yace "yanbiyu ne duk maxa" ciki da jin ddi momy tace "Allah sarki, to ya fateemar?" Abba ya dan yi shiru a sanyaye sae kuma yace "Alhmdllh," momy tace "tohdon Allah ka bata wayar" Abba ya girgixa kai da kyaryace "ni ina waje ne" momy tace "toh shknn, Ashfah ma bata jin ddi wllh amma na kira Mata likita ya xo har ya dubata ya mata allura, daxu muna kitchen ta yanke jiki ta fadi wllh ko minti talatin ba ayi ba ma ynxu, dama kuma tun jiya na lura bata jin ddi, kaga da mun xo" Abba da hawaye kawae yake ya daure yace "to sae na dawo" yana fadin hka ya katse wayar, bbu abinda Ameesha take har lkcn bn da kuka kmr ranta xae fita, dad dinta ya kamo hannunta ya share mata fuskar ta yace "maxa ki tafioffice dina ki xauna, dnt say a word to any body" kaekawae take gyada masa a sanyaye har lkcn tana hawaye, ya kuma share mata fuska snn ta juya jiki ba kwari tana jan kafa ta fita daga ward din, Khaleel ta hango tayi saurin canxa hanya amma tuni ya ganta ya nufo ta da sauri, tayi kmr bata gansa ba ta ci gaba da tafiya da sauri da sauri, bin ta yyi shi ma da sauri har ya risketa ya rikota yace "wait Ameesha, don Allah ta haihu ne?" Ameesha ta ki juyowa ta dake tana ci gaba da tafiya ta ce "ehh ynxun nn ta haihu, sauri nake dad ya aike ni office" juyo da ita yyi da sauri yace "wait, don Allah is she OK" Shiru yyi yana kallonta ganin idanuwanta ynda suka kumbura, ta kirkiro murmushi tana gyada masa kai tace "yes she is OK, amma ta sha wahala ssae, ta ban tausayi" tana fadin hka tayi saurin juya masa baya ta dalilin hawayen da ya shiga taruwa idonta ta ci gaba da tafiya tace "bari in dauko abindaaka aikeni" Khaleel ya kuma bin ta ya juyo da ita hawayen da take mayar wa ya xubo mata lkci daya ta kasa daurewa ta fashe da kuka ssae, tsayawa kallonta yyi yana girgixa kae yace "no, no ki gaya min ina fateema ta, me ya faru" juyawa yyi da sauri ta rikosa cikin kuka ssae tace "wllh she is OK Khaleel, bbu abinda ya sameta" tura ta yyi ganin fuskokin dukka nurses din yasa ya nufi ward din da suke da sauri ya tura kofan ya shiga, kallo daya yyi ma Abba da boss dinsa ya nufi kan gadon da take da sauri dad din Ameesha ya taresa yace "kai ina xaka, me ya shigo da kai nn wat did I yell yhu, so kke ka tashe ta tana bacci," Khaleel ya girgixa kai cikin rudewa yace "No,no no don Allah ku gaya min me ya sami matata me yasa aka rufe ta hka" bae jira amsa ba ya fixge hannunsa da karfi daga rikon da dad din Ameesha yyi masa ya nufi kan gadon da sauri ya cire xanin gadon da aka lullubeta da yana kallonta yace "fateema," ya kira ta ya fi sau goma yaji shiru hkn ya sa ya shiga jijjigata har lkcn yana kiran sunanta a rikice, duk ynda dad din Ameesha ya so janye shi daga wajen bae yiwu ba, jikin Khaleel na rawa ya kama hannunta ya shiga feel dinPulse dinta lkci daya ya fasa wani karan da ya girgixa duk wani mahalukin da ke cikin asibitin, lkci daya kuma ya yanke jiki ya fadi wajen.114.....Allah sarki rayuwa, bbu Wanda bae ji mutuwar fateema ba, tun daga kan kawaye har yan uwa da abokan arxiki ba a mgnr iyayenta, Ummin Khaleel tayi kuka tayi kuka har ta gode Allah, Dad kansa yyi kukan ssae don bae bata mutuwa a lkcn ba, ba a maganan momynta da bata taba xaton mutuwar yartata a lkcn ba, mutuwar ta girgixa ta ba kadan ba tayi kukan tayi kukan tayi haukan har ta gode Allah, da ta tuna ganin yar ta na karshe da daddare da cewan da tayi ta yafe mata sae tayi kuka ba kadan ba, Abba ya fi kowa shiga damuwa, barin idan ya tuna a kan idonsa ta rasu sae ya ji hawaye na xubo masa, Ashfah kam sumanta yyi biyar duk ta xama kmr wata me jinnu kullum sae an mata alluran bacci, wayyo ba a mgnan Khaleel da ke neman bin ta, shi ma din kullum cikin masa alluran bacci ake don komawa yyi kmr wani xautattce, Najeeb ya ji ddin sae da ya nemi gafarar fateema ta bar gidan duniya duk lkcn da ya tuna hka sae yyi kwalla, bbu Wanda ya kai sa tausayin abokin nasa don shi ma ya shiga damuwa ssae kmr matarsa ce ta rasu, hka ma Al-ameen da matarsa, kowa kuka bbu me ba wani baki, sae ka rantse kace yar uwar Zeenat ce ta rasu ynda ita ma Mutuwar ya girgixa ta, ba a mgnr Meenah da suka dan saba, bbu Wanda ya samu courage din daukan yaran ya kula da su bnda Momyn Meenat, ta kwashe su kawae ta kai su gidanta, a hnkli a hnkli ranaku suka dinga ja har Fateema tayi wata biyu cif da rasuwa, amma Khaleel har lkcn an rasa gane kansa, ko ta kan yaran da ta bari baya bi, kullum ba shi da aiki sae tunanin fateemarsa wife dinsa, bbu ranan Allahn da xae wuce da baxae yi kuka ba, gashi yau lfya gobe ba lfya, ssae dad dinsa da umminsa ke tausayinsa, kullum dad ne ke sa shi gaba ya ci abinci ko kadan ne, duk ya rame ssae ba kadan ba, ba shi da aiki saetunani, sau dayawa Abban late Ashnaah kan xo har gidansu ya dubasa, don shi ma mugun tausayinsa yake, ya fi kowa jin mutuwar, wasa wasa har aka yi wata biyar da rasuwar fateema, har lkcn yaranta na gun momyn Meenat sun yi wayo abunsu gasu tubarakalla manya da su duk fateema suke kama da. Lkci lkci momyn meenat kan kai su gidan kakanninsu su gansu, in ta kai su gidansu Khaleel wnn satin, wani sati ta kai su gidansu Abba, ssae Abba ke son jikokin nasa amma ya kasa cewa a bar masa su, ranan wata Sunday Abba yace Khaleel ya xo yana nemansa, da yamma Khaleel ya isa gidan bayan sun gaisa da momy ya shiga falon Abba ya xauna don jiran sa, har lkcn gashi nn gashi nn dae ne, Ashfah ce ta shigo falon rike da faranti dauke daruwa ta ajiye masa ta gaishesa ba tare da ta kallesaba, ya daga kai yana kallonta yyi shiru, a hnkli ya bude baki ya amsa ta bar falon da sauri, lkci daya hawaye suka xubo masa don ta tuna masa da fateemarsa wife dinsa, goge hawayen yyi da sauri jin muryan Abba, ya sauka har kasa ya gaishesa, Abba ya amsa da fara'arsa yace "ya jikin, daxu dad din ka ke ce min baka ji ddi ba jiya" Khaleel ya sunkuyar da kansa yace "da sauki Abba"115.....Abba ya dan yi shiru snn yace "dama wata shawara na yanke Ibrahim, Allah yasa xaka amince da ita" Khaleel ya dago kai yana kallonsa bae ce komae ba ya kuma dukar da kansa, Abba ya numfasa yace"Na yanke shawarar hada ka da yar uwar marigayiyane, Allah yasa xaka so hkn Khaleel," Khaleel ya dagokai lkci daya hawaye suka shiga xubo masa a hnkli yana girgixa kai yace "A'a Abba ni baxan sake aure ba, fateema ce kadae matata a duniya...." Kasa ci gaba yyi ya rike kansa yana hawaye ssae, Abba yyi shiru yana kallonsa cike da tausayinsa, a hnkli yace"abun da yyi fateema shi yyi khadija, hasalima rana daya suka fito duniya don hka ka dauki khadija a matsayin fateema na baka ita halak malak, ni xan biya maka sadaki bayan shi kuma ba ma bukatar komae, amma ina son ka min alfarma daya Khaleel," Khaleel ya dago kai yana kallonsa har lkcn yana hawaye, Abba yace "ina son ka bani daya dagayaran naka in rike ko hkn xae dinga debe min kewar fateema, in nuna masa son da ban nuna ma uwarsaba, don ita son boye na mata" Khaleel ya gyada kae da kyar yace "na baka Abba" Abba yyi murmushin jin ddi shi ma hawayen cike idonsa yace "toh ngdd Khaleel, amma kayi shawara da iyayenka, tashi ka je Allah yyi maka albarka" Khaleel ya mike da kyar yyi masa sallama ya fita daga gidan, yana fita Abba ya jinginar da kansa jikin kujera, lallai Allah ya nuna masa ishara, rabon sae fateema ta bar masu mata addu'a xata bar duniya ne ya janyo komae, don ko da abubuwan nn basu faru ba wa'adin da Allah ya dibar mata a duniya knn, lallae Allah da iko yake, Ashfah ya kira ta shigo falon ta xauna kasa tace"Abba ga ni" Abba yana kallonta yace "ba ki taba tsallake duk wani umarnin da na maki ba khadija, duk abinda xae faranta Mani rae kike yi, wnn karan ma bana fatan xa ki tsallake" Ashfah tayi shiru bata ce komae ba, Abba yace "ina son hada ki aure da Khaleel ne khadija," dago kai tayi da sauri tana kallonsa sae ga hawaye can kuma ta fashe da kuka tana girgixa kai tace "Wayyo Abba don Allah kayi hkuri ni baxan iya auren mijin yar uwata ba" Abba yyi shiru yana kallonta, sae kuka take ssae, a hnkli Abba yace "do dat for my sake dota, nd for the sake of the kidz she left, baxa su taba rashin uwa ba, xa ki daukesu ne tamkar ke kika haifesu" ssae jikin Ashfah yyi sanyi bbu abinda take sae kuka, Abba yace "tashi ki je, Allah yyi maki albarka" ta mike da kyar tana kuka ta nufi sama, da kyar ta iya gaya ma momynta abinda Abba ya gaya mata, momy tayi murmushi ta rungumeta tace "do dat for d sake of the kidz dota"Bayan sati biyu aka daura auren Ashfah da Khaleel, don kowa ya ji ddin shawarar da Abba ya kawo bariniyayen Khaleel, Abba ne ya biya sadakin kmr ynda yace ya kuma yi mata kayan daki da komae, a ranan kuma aka kai ta gidan mijinta Khaleel da dad dinsa ya mallaka masa halak malak. Bbu abinda take bnda kuka har aka watse aka bar ta ita kadae, gani take kmr ta ci amanar late sis dinta, Karfe tara da rabi Khaleel ya shigo gidan rike da twinz dinsa a hannu da wani leda, yan kwanakin nn kam suna samun kulawan ubansa ssae sabanin da da ko kallonsu baya yi, dakin da Ashfah take ya nufa a sanyaye ya tura kofar tare da yin sallama can ciki ya shiga, kasa amsawa tayi har lkcn tana hawaye, ya kwantar da yaran hannunsa kan gadonta suna ta wasa abunsu, snn ya fiddo feedernsu da madara da ke cikin ledan ya ajiye a kasa, ya bude daya ledan ya ajiye mata a hnkli yace "ga abinci nn na siyo maki" yana fadin hka ya juya ya fita daga dakin. Ashfah ta daga kai tana kallon yaran da ke ta wasa abunsu kan gadon hawaye na bin kuncinta. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar116.......Ashfah ta kusa awa daya a xaune gefen yaran tayi tagumi tana kallonsu, mikewa tayi a hnkli daga karshe ganin sun fara bacci, ta gyara masu kwanciya snn ta cire kayan jikinta ta canxa xuwa gown na bacci, ledan da ya ajiye mata ta dauka ta bude fridge ta ajiye, snn ta dauki hijab ta sa tayi kwanciyarta gefen yaran. Can cikin dare Sultan me sunan Abbansu Ashfah ya farka ya fara kuka, lkci daya ya tada dan uwansa Sudais me sunan dad, suka hadu suka dinga kuka, Khaleel na xaune kan darduma ya idar da sllhn Nafila ya ji kukansu, sun fi minti goma suna kukan, Khaleel ya mike jin kukan nasu sae karuwa yake yana kallon agogo ya ga Karfe biyu saura, kofa ya nufa ya bude ya fita ya nufi dakin Ashfah, ya dde tsaye bakin kofar daga karshe yyi sallama yana tsaye bae shiga ba, sallama ya kuma yi, jin bata amsa ba yasa ya tura kofar a hnkli ya shiga dakin, ga mmkinsa kwance yasameta tana bacci ga yaran gefenta sae rusa kuka suke har da shure shure, kasa daina kallonta yyi yana ganin ta kmr Ashnaahr sa gashi exactly irin kwanciyar Ashnaah tayi, ya karaso gadon a sanyayeba tare da ya san lkcn da yyi hkn ba har lkcn idonsa a kanta, hawaye ne suka cika idonsa lkci daya xuciyarsa ta raya masa ba fa fateemarsa bace wnn wata ce daban kawae kama suka yi, juyawa yyi da sauri hawaye na sakko masa ya nufi kofa xae fita jinkukan yaransa ya sa ya dakata a bakin kofar ya juyaa hnkli yana kallonsu, share fuskarsa yyi ya karasa gadon ya dauki sultan dake kusa da ita, sae a snn Ashfah ta farka a dan firgice ta mike xaune da sauri tana gyara hijab dinta ta koma baya tana mitsika ido, Khaleel dae bae ce mata komae ba ya dauki duk yaran yana lallashinsu, Ashfah tayi mmkin irin baccin da tayi don rabonta da bacci irin hka tun kafin Abba yace xae hadata da Khaleel, kullum cikindare bata da aiki sae na kuka da tunane tunane, mikewa tayi da sauri ba tare da ta kallesa ba tace"in hada masu madara ne?" Shi ma bae kalleta ba yace "eh" ta fita da sauri daga dakin ta shiga neman kitchen don samo ruwan xafi, Eva water ta daura a gas ya dan yi xafi snn ta dawo dakin ta shiga hada masu madaran cikin feedern su, tana gamawa ta mika masa daya feedern tace "kawo dayan in basa" ya mika mata sudais ta karbe shi ta xauna gefen gadon ta shiga basa feedern, Khaleel kam bae xauna ba daga tsayen da yake ya shiga ba Sultan dake rungume jikinsa, lkci daya yaran suka koma bacci, Ashfah ta kwantar da Sudais da ke hannunta a hnkli, shi ma ya kwantar da Sultan gefen Sudais ba tare da ya kalleta ba yyi mata sae da safe ya fita.Washegari da safe Ashfah ta rasa ta ynda xa tayi ma yaran wanka, ga dae ruwan xafi ta sirka a bayi amma bata san ta ina xa ta fara wankan ba don gunMomyn Meenah yaran suke tun suna jarirai, ta fito daga bayin a sanyaye ta xauna gefen gado tana kallon yaran da ke ta wasa abunsu, a hnkli ta shiga cire masu kayan jikinsu gaba daya har ta gama snn ta dauki Sultan ta nufi bayin da shi tana kallon ruwan dake sirke cikin bahon wankansu kmr xata yi kuka, ga sabulu da soso ta ajiye gefe, Muryar Khaleel ta ji a bayanta ta juya da sauri ta rungume yaron a jikinta don har lkcn nyt gown ne jikinta, ya kauda kai yace "xa ki iya masu wankan ne" ta juya masa baya tayi shiru, a hnkli tace "ni ban iya ba" yace "OK kawo in masu" juyawa tayi ta mika masa yaron hannunta ta fice da sauri ta je ta sa hijab dinta, shi yyi masu wankan gaba daya ya shirya su, ita kuma ta hada masu abincin su ya ba daya ita mata ba daya. Hka Ashfah ta wuni ranan daga ita sae twins a daki gashi basu da rigima ko kadan sae in sun ji yunwa, Rukayya ce ta kawo masu abinci throughout ranan, Khaleel kam na dakinsa tun bayan da ya taimaka ma Ashfah ya shirya yaran bae kuma fitowa ba yana aikinsa da ya saba kullum na tunanin Ashnaah, bbu ranan Allahn da baxae wuce ba da baxae bata awa biyu xuwa uku cikin lkcn sa ba yana tunanin irin rayuwar da suka yi tun daga farkon haduwarsu da Ashnaah har xuwa rananda xata bar duniya, hkn kan sa shi kwalla ba kadan ba, kullum Addu'arsa bae wuce na Allah ya rahama mata ba ya bata gidan aljanna, Da daddare Rukayyana komawa gida bayan ta taimaka ma Ashfah ta yi ma yaran wanka Khaleel ya shigo dakin da sallama ya tsaya daga bakin kofa yace "bbu matsala ko?" Ashfah ta gyada masa kai ya juya ya fita tare da yi mata sae da safe ya rufe masu kofar.Satin Ashfah biyu knn gidan Khaleel amma ko gaisuwa baya hadata da shi in ka ga sun yi magana to ya shigo daki taimaka mata ya basu abinci in ya jisun hade mata kae suna kuka ne ko kuma ya taimaka mata ya wankesu da safe don sun ma daina tashi cikin dare in har suka koshi da daddare, shknn iyakar abinda ke hadasu knn, kwata kwata ya daina yini a gida ynxu, ita dae bata san inda yake xuwa ba amma da Karfe shidda yyi xae dawo gida da yan kayan ciye ciye ya ajiye mata, tuni ta fara girki a gidan kuma duk girkin da xata yi xata xuba masa nasa ta ajiye kan dinnin kuma yana ci ba laifi idan ya dawo, wani lkcn yace mata "thank yhu" in yashigo taimaka mata da twinz, ita dae bata cewa komae. Yau da daddare Ashfah na gama shirya su sultan da daddare ta basu abincin su suka yi bacci lkci daya ta kwantar da su, ynxu kam ta fara sabawada iya rainansu ita kadae ba sae an taimaketa ba, sae dae tana shan wahala ssae don rainon yan biyu ba abu me sauki bane da daya ya fara kuka daya zae amshe ko wasa yake su hadu suyi tayi duk su rikitata wataran ma ita ma ta sa masu kukan, ssae take son yaran kmr xata hadiyesu, tana kwantar da su ita ma ta kwanta nn da nn bacci ya dauketa, can cikin dare suka tashi gaba daya suka fara kuka, ta mike xaune da kyar tana kallonsu don da wuya ka ga sun tashi cikin dare ynxu gashi ba su barta tayi baccin rana ba ranan, kan fridge ta nufa ta dauko Goran ruwansu don tasan ba yunwa a tare da su saedae kila kishin ruwa amma kmr ta kuma sa su kuka da ta basu ruwan, ta shiga hada masu madara da sauri, ta daukesu a tare tana basu nn ma suka ki karba kmr sun hada baki, sae kuka suke, ita ma ta fashe da kuka tana kallonsu tace "toh me ku ke so?" Tura kofar da taji anyi tare da sallama yasa ta dauki hijab dinta da sauri ta sa, ya karaso cikin dakin yanakallon twins din ya duka ya dauki sultan snn Sudais duk ya rungumesu yana lallashi, jin basu yi shiru ba yasa ya xauna gefen gadon ya dauki feeder yana basu, nn ma dae ba su wani karba ba, ya gane to kila basu da lfya ne, yan dubaru yyi masu ya basu magunguna, yana ta lallaba su har dae ya samu duksuka koma bacci, daya a kafarsa, yana rungume da daya kuma, juyawa yyi yana kallon Ashfah ya ganta xaune can karshen gadon wae don ya xauna gefen gadon, ta jinginar da kanta jikin gadon tana bacci daga xaunen da take, duk lkcn da ya kalleta sae gabansa yyi mugun faduwa lkci daya kuma Ashnaah ta fado masa gashi yana ddewa kafin ya daina tunaninta, meyasa xa a basa mata me kama da fateemarsa hka, juyawa yyi ya kuma kallonta jikinsa a sanyaye yace "ki kwanta" bae ga alamar ta san yana yi ba don da gani tayi nisa da baccinta, ya mike a hnkli ya nufi dakinsa da yaran gudun kar su tashi duk ya kwantar da su a dakin snn ya dawo dakin Ashfah ya kuma ce mata ta kwanta daga bakin kofar da yake tsaye amma shiru, yw fi minti biyar a tsaye snn ya karaso cikin dakin ya dan buga gado ko xata tashi nn ma bata tashi ba, but ko kadanAshnaah bata da nauyin bacci hka da ta ji motsi take farkawa, ya dan yi murmushi jikinsa a sanyaye ya dan dafata.117.....A tsorace Ashfah ta farka tana kkrin mikewa ya koma baya da sauri yace "No nace ki kwanta ne" mikewa tsaye tayi ta koma jikin gado kanta a kasa, ya juya da sauri ya nufi kofar xae fita, da sauri tace"yaran fa" ganin bata gansu kan gadon ba, ba tare daya kalleta ba yace "suna daki na" yana kai wa nn ya kulle mata kofarta. Washegari Ashfah ta gama shirin ta da safe ta gyara dakin ta snn ta sauka downstairs don hada break fst, ko da ta gama har tara yyi, ta haura sama don komawa dakinta taji kukan su sultan, kasa shiga dakinta tayi ta tsaya bakin kofa, don da taji kukansu hnklinta ke tashi ta rasa sukuni barin ynxu da tasan ba su ci abinci ba tun wayewar gari, can dae ta gaji da tsayuwa ta shiga dakinta, ta fi minti biyar da shiga amma har lkcn sae karuwa kukansu yake, ta kasa daurewa ta mike kmr xata yi kuka ta fita da sauri ta nufi dakin, tana shiga dai dai lkcn da Khaleel ke fitowa daga wanka knn daure towel a waist, da sauri ta juya masa baya a mugun tsorace sae kuma ta nufi kofa ta fice daga dakin da sauri har tana tuntube, Khaleelya dauki yaran yana lallashinsu har suka yi shiru snn ya xaunar da su tunda sun fara iyawa ynxu cikinkekunansu da fanz suka kawo masu as gift ranan da aka rada masu suna bayan rasuwar uwarsu duk da ba ayi wani taron suna ba, cikin minti sha biyar ya gama shirin sa ya kwashi yaran ya kai mata ba tare da ya kalleta ba yace "anjima xa mu fita, ki hada masu kayansu," yana kai wa nn ya juya ya fita, Karfe sha daya suka bar gidan gaba daya da kayan sawansu da ta harhada masu da madaransu da feeder, bayan mota ta xauna da yaran a jikinta, ga mmkinta gidansu ta ga Khaleel ya nufa, yana gama parkin suka shiga a tare, sae murna take xata ga Abbanta da momy, momy tayi farincikin ganinta hkama Abba, inna ma na gidan ranan, inna ta rungume jikartata tana mata sannu da xuwa da daya daga yan biyun hannunta, sae da Ashnaah ta rasu da sati biyu aka sanar da inna da ke can katsina lkcn, ba sae na fadi tashin hnklin da ta shiga ba don dagewa tayi kan Abba ne ya kasheta ba kowa ba wllh, da kyar dae aka samo kanta don sae da ita ma tayi yankwanaki a gadon asibiti don ba karamin girgixa ta mutuwar tayi ba, Khaleel da ya biyo bayan Ashfah rike da Sudais a hannu ya duka har kasa ya gaida innar da ba wani sake masa take ba don a xaton ta shine sanadin faruwan komae, sae da duk suka bar falon ya rage shi da Abba snn yace "dama Abba sultan na kawo maka, na baka shi kmr ynda ka bukaci inyi hkn idan Allah ya yrda," Abba yyi murmushi yace "Ma'sha Allah, Allah yyi maka albarka Khaleel na gode kwarae da gske" Khaleel yadukar da kansa yace "Ameen Abba, Sudais kuma xan kai sa can gidanmu gun Ummina" Abba yace",Allah sarki, Allah dae ya raya su ya albarkaci rayuwarsu" Khaleel yace "Ameen Abba" Ashfah duk a tunaninta karatu xata koma shiyasa aka maido yaran gidansu amma har suka fara shirin tafiya bataji Abbanta yyi mata mgnr karatu ba, hkn yasa hnklinta ya tashi, Karfe biyu suka bar gidan, Khaleel ya kai Sudais can gidansu kmr ynda yace, dad dinsaya kira sa har bedroom dinsa yace "alfarma daya nake son ka min ynxu son" Khaleel ya daga kai yanakallonsa, Abba ya nisa yace "ko sati ba ayi ba da xuwan Alhaji Mukhtar wajena, so nake kayi hkuri ka mance duk abinda ya faru ka koma bakin aikin ka, shi ya nemi wnn alfarman daga gareni kan cewa in maka mgna xaka fi ji" Khaleel yyi shiru bae ce komae ba, ko kadan badan mahaifin sa ne yyi masamgna ba bbu abinda xae maida sa asibitin nn, but he vowed never to disobey his father till his lst day on earth, a sanyaye yace "to xan koma In'sha Allah dad, nagode" Dad yyi murmushi yace "toh Allah yi maka albarka, ya raya maka yaran ka ya albarkaci rayuwarsu, ya baku xan lfya da hkuri da matar ka" Khaleel yyi murmushi a sanyaye yace "Ameen Dad" snn ya mike yyi ma Dad dinsa sallama yace xa su tafi, dakin Ummi ya tarda Ashfah yace ta taso su tafi, Ashfah ta mike da kyar tana kkrin mayar da hawayen idonta ganin Sudais ma nn xa su bar shi, ita kuma abu kadan ke sa ta kuka ba kmr Ashnaah ba, sallama tayi ma Ummi, Ummi ta rakosu har downstairs Ashfah tayi ma dad ma sallama suka fita Khaleel na biye da ita a baya, rasa inda xata xauna a motar tayi, ta bude bayan motar a hnkli ta shiga, shi dae bae ce mata komae ba ya shiga driver seat ya tada motar suka bar gidan, Karfe goma saura suka isa gida, Ashfah ta nufi dakinta da sauri ta dinga rusa kukan rabata da su sultan da akayi, shknn ita kadae xa tayi ta xama kmr mayya a gidan bbu me debe mata kewaye, gajiya tayi da kukan ta mike xaune a sanyaye ta cire kayan jikinta ta daura xani ta shiga wanka, ko da ta fito gown din baccinta kawae ta xura ta kwanta ta ci gaba da kukanta, sha biyu saura Khaleel ya tura kofar dakin a hnkli tare da yin sallama ya shigo, Ashfah ta mike xaune da sauri tana share hawayen fuskarta lkci daya ta shiga dudduba inda hijab dinta yake amma ta kasa mikewa ta dauko don kayan baccin jikinta karami ne, bata taba tunanin shigowarsa dakin a lkcn ba, Khaleel ya karaso kusa da ita ya xauna gefen gado yana kallonta, sunkuyar da kai tayi da sauri gabanta na faduwa, ya dago kanta a hnkli yace"kukan me kike khadija" da ganinta kasan a tsorace take, ta saukar da idonta muryarta na rawa tace "su sultan...." Sae kuma ta fashe da kuka, Khaleel ya lumshe ido ya rungumeta murya can kasa yace "kiyihkuri xa su dinga xuwa maki hutu" Ashfah da ta gama tsorata don tun da take bata taba jin ta a kirjinNamiji ba ta shiga kkrin kwace kanta, ya saketa da sauri ya mike kmr wnda ya tuno abu juyawa yyi ya fice daga dakin yana kkrin mayar da hawayen idonsa.Washegari da safe Ashfah na gama hada break fst ta dawo dakin ta kwanta, Karfe goma saura ta ji fitarmotar Khaleel, sae da ya fita da kusan awa daya snn ta sauka downstairs, dinnin ta nufa don sae yyi break ita ma take yi, taga yyi ba laifi, ta ja kujera ta xauna ta shiga hada tean ta, Khaleel kam clinic ya nufa don amsa kiran da dad din Ameesha yyi da safe ba don ransa ya so ba sae dan darajar mahaifin sa. Da kyar ya iya shiga asibitin jikinsa a sanyaye tunowa da yyi a cikin nn wife dinsa ta rasu, tunanin hkn yasa kwalla taruwa cikin idonsa ya nufi office din boss din nasa bayan sun gaisa da nurses da ke reception, Da farko hkuri dad din Ameesha ya soma basa kan abubuwan da suka faru a baya snn ya bukaci da ya koma bakin aiki a ranan, Khaleel yace "Dad sae dae ko gobe, bn sanar da iyalina xan tafi gun aiki ba," dad din Ameesha yace "toh bbu matsala, Allah ya kai mu goben" Khaleel ya mike yyimasa sallama ya fita, a haraban asibitin suka hadu da Ameesha, ta gaishesa da fara'arta ya amsa yana murmushi snn tace ya gaida mata Yara ta nufi cikin asibitin.118.....Sae da dad din Ameesha ya kuma kiran Khaleel snnya shirya ranan wani Monday ya tafi clinic, satin sa daya da komawa aiki ranan Najeeb ya samesa office dinsa, Najeeb ya ja kujera ya xauna don tun ranan ba su haduwa ba suka gaisa snn ya tambaye shi ya khadija, Khaleel yace "tana lfya qlau" duk da ya fi sati bae ma sa ta a ido ba, kallon abokin nasa Khaleel ya tsaya yi, yyi mugun mmkin rashin nuna damuwarsa kan hada aurensu da aka yi da Ashfah don ya san yana sonta ssae, amma dae bae taba cemasa komae ba, Najeeb yace "Came to ask for yhurforgiveness frnd, Allah yasa xa ka iya yafe min" Khaleel yyi shiru yana kallonsa don bae gane inda xancensa ya dosa ba, Najeeb ya fiddo wata takarda daga aljihunsa ya mika masa, Khaleel ya karba yana warware takardan, idonsa ya sauka kan content din jikin takardar, Khaleel ya karanta ya fi sau biyar a xuciyarsa ga mmkinsa kuma rubutun Najeeb ne, Khaleel ya ce "wat about this, wats d meaning?" Najeeb yace "yhu remember dat day I forced yhu to birthday party of Maska?" Khaleel dae yyi shiru bae ce masa komae ba, Najeeb ya ci gaba"I got yhu drunk, yes I did! I made yhu recopy dis content to another paper while being drunk, yes I did! And that was hw everything started" kallonsa kawae Khaleel yake da mugun mmki, Najeeb ya ci gaba a sanyaye, "nasan idan ba proof din nn na kawo maka ba baxa ka taba yrda ni na rubuta takardan ba na baka kayi recopyn, frnd forgive me plss nd give me a second chance, I am vry happy dat sai da na roki gafara gun fateema a ranan da xata rasu, kuma tace ta yafe" Khaleel ya gyada kai ahnkli duk da irin tafarfasar da xuciyarsa take yace"And all dis happened as a result of???" Najeeb yyi shiru yana kallonsa , Khaleel yyi murmushin takaici yace "Shan giya! don hka duk wani mashayin giya yyi hasara I get dat, in my next life idan da akwae knn bbu abinda xae kuma hadani da giya, nayi da nasanin sanin giya da fara shan shi, its nt ur fault though Allah ne ya nuna min ishara" Khaleel na kai wa nn ya mike ya fice ya bar masa office din hawaye cike idonsa, sae da yyi kusan sati biyu yana avoidin din Najeeb, Najeeb na bin sa har daga karshe Khaleel ya gaji yace toh ya kai proof din ya nuna ma parent dinsa ya wanke xargin da ake masa, hka kuwa Najeeb yyi yaje ya sami dad din Khaleel yyi masa bayanin komae bbu shakka, dad din Khaleel ya tasa shi gaba suka je gun Abba yyi masa bayani da kansa, ssae jikin Abba yyi sanyi bbuabinda ya iya cewa sae Allah shi kyauta, dad ya kira Khaleel bayan ya koma gida yace "baya son kuma ganinsa da Najeeb" Khaleel ya amsa masa kawae ba don xae iya yin hka ba. Yau satin Khaleel biyu rabonsa da ya daura ido kan Ashfah kullum da safe yake fita baya kuma shigowa gidan sae bayan isha, sae dae kuma duk wani abun da yasan xa ta bukata yana siyo mata ya ajiye mata kan dinnin, yau ma kmr kullum sae bayan isha ya shigo gidan, yana haurawa sama ya ji shesshakar kukanta, har xae shiga dakinsa sae ya fasa don lkci daya hnklinsa ya tashi ya nufi kofar dakinta ya tura tare da sallama ya shiga, xaune ya sameta kasa ta hade kae da gwiwa tana kuka, tana jin an bude kofarta ta dago kai da sauri, kasa karasowa cikin dakin yyi jikinsa yyi sanyi ssae lkci daya Ashnaah ta fada masa in dae ya ji kukanta to a irin wnn yanayin yake shigowaya sameta, Ashfah ta shiga goge hawayen fuskarta ba tare da ta kallesa ba ya karaso cikin dakin yana kallonta ya duka gabanta a hnkli yace "Me ya faru khadija" shiru tayi bata ce komae ba ta sunkuyar da kanta, ya dago fuskarta yana kallon idonta da yyi ja ssae a sanyaye yace "ki gaya min plss, kina son wani abu ne" ta fashe da kuka bata ce komae ba, dagota yyi ya xaunar da ita gefen gadon ya xauna shi ma, taki Bari su hada ido, ya kuma dago fuskartayace "ki gaya min damuwarki don Allah" kin cewa komae tayi, ya gaji da tambayarta ya mike a sanyaye ya bar dakin. Kasa bacci khaleel yyi cikin dare, don duk ta daga masa hnkli tunda bae san me ke damunta ba, daya da kusan rabi ya mike da kyar ya fita daga dakinsa ya nufi nata.love yhu ol Fanz. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 119..... Kwance Khaleel ya sameta idonta biyu, tana ganinsa ta mike xaune da sauri ta jawo hijab dinta ta sa, ya karaso ya xauna gefenta yana kallonta a hnkli yace "kin ki gaya min damuwar ki khadija, tell me plss" sunkuyar da kanta tayi da sauri, ya dago fuskarta wasu sabbin hawaye suka shiga sakko mata, rungumeta yyi ya rufe ido, ta fara ja da baya da sauri ya ki saketa a hnkli yace "sae kin gaya min damuwar ki" jikinta na rawa tace "kai na ne ke min ciwo" kin saketa yyi har lkcn ya dago fuskarta ya dafa goshinta ya ji bbu xafi, ya girgixa mata kai yace "yhu re nt telling d truth" sunkuyar da kanta tayi da sauri har lkcn hawaye na sakko mata, ya kwantar da ita a hnkli kan faffadan kirjinsa, lkci daya jikinta yyi sanyi shi ma hka, sun fi minti goma a hka jin ta sauke ajiyar xuciya yasa ya dago fuskarta ya ga har ta yi bacci, a hnkli ya kwantar da ita, ya dafe kansa Ashnaah kawae yake tunawa, a sanyaye ya mike ya fita daga dakin, tun daga ranan ya daure ya daina avoidin dinta dama a da gani yake kmr ya ci amanar Ashnaah idan yace xae yi xaman aure da yar uwarta, duk safiya kan ya fita ya kan shiga dakin yace mata ya tafi, da daddare kam idan ya dawo ya daina ajiye mata duk abinda ya siyo mata a dinnin table kmr ynda ya saba, ynxu kam sae dae ya kai mata daki, amma stil taki sakin jiki da shi, a ynda ya Lura ma kmr tsoronsa take, ko idonta biyu pretending take tayi bacci idan ya shigo dakinta da daddare, shi dae sae dae ya ajiye mata ya fita, kusan duk bayan sati biyu ya kan kaita gida ta gaida su Abba daga can su tafi can gidansu gun Ummi, duk don ta ji ddi ta kwantar da hnklinta amma kullum jiya e yau, bbu abinda ke damun Ashfah yake sa ta kuka ko da yaushe irin daina xuwa sch din da tayi, kullum kmr mayya ita kadae a gida daga dare har safe gashi an rabata da su Sudais, amma ta kasa samun courage din yi ma Abba magana yyi ma Khaleel din mgna ya bar ta ta ci gaba da karatun ta, ranan wata Sunday tana kitchen tayi nisa cikin tunanin da take har shinkafar da ta daura ya soma konewa bata sani ba, Khaleel da ke garden ya dinga jin kaurin shinkafa ya Mike da sauri ya shigo gidan ya nufi kitchen, xaune ya sameta tayi tagumi, tana ganinsa ta Mike tsaye da sauri, ya kashe gas din yana kallonta da mmki, karasowa yyi kusa da ita ta shiga komawa baya da sauri, ya kamo hannunta suka fito daga kitchen din ya koma falo da ita, xaunar da ita yyi kan kujera ya xauna yana facing dinta, a hnkli yace "me ke damun ki khadija, kiyi hkuri ki gaya min don Allah, ko kina son in hada ki da Abba ne" girgixa masa kai tayi da sauri hawaye ya shiga bin kuncinta, murya can kasa yace "ko kina son ki koma karatu ne?" Ta dago da sauri tana kallonsa, lkci daya ta gyada masa kai, murmushi yyi yana kallonta, ta sunkuyar da kai ita ma tayi murmushin a kunyace, a hnkli yace "to kar ki damu xa ki ci gaba" a sanyaye kmr xata yi kuka tace "ngdd" mikewa yyi yace ta je ta ci gaba da abinda take shi kuma ya haura sama, ba karamin farin ciki Ashfah tayi ba don kusan watan ta daya da sati biyu knn rabonta da sch , Washegari kam da kansa ya kai ta makaranta da safe xae fita aiki, tun daga lkcn ta dawo nml, kullum in ya kaita da safe driver ne ke xuwa daukanta idan ta gama lecture, ranan da daddare ya shiga daki ajiye mata abinda ya siyo mata ya sameta tayi shiru bata karatu kmr ynda ya saba shigowa ya sameta, its either Qur'an ne a hannunta ko text buk din Chem, ya karasa kusa da ita ya duka gabanta yana tambayarta me ya faru, kmr xata yi kuka tace "assignment aka bamu kuma bani da wayar da xan yi browsing" yyi shiru yana kallonta snn yace "wani course wae kike yi" tace "Pharmacy" ya wara ido yace "level nawa ynxu?" Tace "300 lvl nake ynxu" yyi murmushi yace "dats nyc, kawo assignment din dakina kiyi a computer" tayi masa gdya cike da jin ddi tayi ynda yace mata, tun daga ranan da an bata assignment dakinsa take xuwa yi, wasa wasa har suka fara sabawa da Khaleel, duk da Ashfah ba da son ranta hkan ke faruwa ba don gani take kmr cin amanar yar uwarta xata yi, da taimakon huduban da momy ke mata kan ta rike mijinta da kyau ta bar tunanin komae a ranta yasa ta sake gaba daya, duk assignment din da bata gane ba ko kuma karatun da bata gane ba shi xata kai ma da daddare ya koya mata, duk irin ynda yake so ya dan dinga ja mata da baya shima don da ya ganta Ashnaah ya ke gani samun kansa yyi da kasa yin hkan, cikin watannin da basu wuce hudu ba suka yi mugun sabawa, har hira tana masa, sae dae yyi ta murmushi yana kallonta, halinta gaba daya sak na Ashnaah ne har da ynda take mgna da dariya, barin idan ta wara manyan idanuwanta exactly na Ashnaah, sae dai ita bata da tsiwa ko kadan ga shegen tsoro uwa farar kura gashi abu kadan ke sa ta kuka, uwa uba ga shegen shagwaba har da na siyar wa, a hnkli a hnkli Khaleel ya soma sakin jikinsa gaba daya da ita don da dari dari yake, wataran har assure din kansa yake Allah ne ya basa second Ashnaah, komae tare suke yi a gidan in har yana nn, har abinci suna ci a tare. Ranan wani Saturday sun dawo daga dinner din bikin Zeenat da daddare wajajen Karfe sha daya yana falo yana kallo ita kuma tana dakinsa tana assignment ya ji ihunta, mikewa yyi da sauri gabansa ya fadi ya nufi sama da sauri don ganin me ya sameta, a bakin kofar dakinsa suka ci karo da ita, dai dai nn aka dauke wuta gaba daya, ta rungumesa ta fashe masa da kuka, a rude yake tambayarta me ya faru, taki basa amsa sae kuka take ba kakkautawa, wayarsa ya ciro da sauri ya kunna fitila ya shiga haska ta don ganin ko abu ne ya sameta gashi taki sake shi, ya ga ba komae, yana rungume da ita suka shiga dakin yana haska ko ina, bae ga alamar komae ba, yace "don Allah ki gaya min menene?" cikin kuka tace "Ashe horror film ka sa min ka tafi koh?" Kasa ce mata komae yyi sae kallonta da ya tsaya yi, ta kuma fashewa da kuka, bae ce mata komae ba ya nufi gefen gado ya xauna ita ma ta xauna kusa da shi kmr xata shige jikinsa tana kuka, sun fi minti goma a xaune snn yace "dama sbda wnn abun kika daga min hnkli hka khadija" shiru tayi kmr xata yi kuka tana kallonsa, yace "kin gama assignment din" ta gyada masa kai kawae, yace "toh sae da safe ki tafi daki ki kwanta" ta wara manyan idonta kmr xata yi kuka tace "ka ga abinda na gani ne" sae kuma ta saka kuka tace "ni wllh baxan iya xuwa ba tsoro nake ji" ya mike yace "toh ki kwanta a nn, bari in je in kashe kayan kallo a falo," ta mike da sauri tace "baxa a kunna gen ba?" Yace "ynxu xa su maido wutan ae" kin tsayuwa tayi ita kadae a dakin ta bi sa suka sauka falo ya kashe kayan kallo snn ya rufe gidan suka koma sama, kwanciyarsa yyi can karshen gado yace "idan kin kwanta ki kashe fitilar wayan," bata ce masa komae ba ta Mike tana Satan kallon sa ta ga baya kallonta, ta cire hijab din jikinta don duk irin sabawar da suka yi bata tsayuwa gabansa ba hijab, ta ajiye hijab din snn ta shige cikin bargo tayi kwanciyarta, jin ta kwanta bata kashe fitilar wayan ba yasa ya juya yana kallo ta ya ga ajiye wayar tayi tsakiyarsu, dauke wayar yyi ya kashe fitilan ta mirgino kusa da shi da sauri ta saka kuka tace "sbda me xa ka kashe min?" Khaleel ya lumshe ido da kyar yace "sbda bna kwana da haske, kuma so kike charge dina ya kare?" Shiru tayi bata ce komae ba ta kuma matsowa kusa da shi a hnkli har yana jin dumin jikinta da saukan numfashinta a jikinsa, bayan minti kusan goma ya gane tayi bacci ganin ynda ta sake masa jiki, tuni jikinsa yyi sanyi hnklinsa ya soma gushewa, ya juyo a hnkli yana facing dinta, kallonta kawae yake cikin idon, ya lumshe ido a hnkli ya rungume ta tsam ya daura bakinsa kan nata, a tsorace ta farka xata kwala ihu yana ganin hka ya saka bakinsa cikin nata, daren nn da daga cikin dare biyun da Khaleel baxae manta ba a rayuwarsa, dare na farko shine daren da ya fara sanin Ashnaah, na biyu kuma shine wnn da ya fara sanin Ashfah, Ashfah ta ba sa tausayi ssae don bata wani bashi wahala ba, ga shi ba karamin daurewa tayi ba duk da tayi kuka ssae amma ba mae sauti ba, abu biyu ya sa ta kuka ba kadan va, na farko gani take kmr ta ci amanar yar uwarta, na biyu kuma axaba, a daren ya taimaka mata ta shiga ruwan xafi don ta samu relieve yana kwantar da ita nn da nn bacci ya dauketa. Shi ma ya dde bae yi bacci va kuma yyi hawaye ssae, don shi ma gani yake kmr ya ci amanar Ashnaah, sllhn da ya dde yana yi cikin daren ya sa ya samu nutsuwa cikin ransa ya yrda da kaddara ya kuma yrda da cewa Ashnaah ta var duniya va dawowa xata yi va tsakaninta da shi ynxu Addu'a, sae wajen Karfe uku ya samu ya rintsa, hkn yasa ya makara tashi yyi sllh da Asuba don har an tada sllh ya farka, yyi alwala da sauri ya fita don xuwa masallaci, ko da ya dawo da mmkinsa gyaran dakin ya tar da Ashfah na yi, sae tayi mugun basa tausayi, ya karaso kusa da ita yana kallon idonta da ya kumbura don kuka ta sunkuyar da kanta da sauri, a hnkli yace kin yi sllh ne?" Ta gyada masa kai kawae, ya rungumeta hawaye cike idonsa yace "am srry wif... Kin karasa word din yyi, yyi saurin cewa dear. 120...... 5 years ltr Ashfah ce kwance falo tana fama da laulayin sabon cikin da ke jikinta, ga twins dinta mata sun sa ta gaba sae damunta suke, daya me sunan Ashnaah ana ce mata Afrah daya kuma me sunanta ana ce mata Amrah, bbu abinda suka bari nata da Ashnaah, sultan da Sudais ma na gidan ranan da yake lkcn hutu ne, ynxu kam sun xama samari shekarunsu shidda da watanni a duniya, Khaleel kuma na kitchen yana hada ma yaran gaba da cornflakes don ba girki Ashfah ke iya yi ba, ynxu kam komae ya dawo masu nml a family din soyayyarsu me burgewa suke yi da khaleel da ke jin kmr xae mai da ta ciki, 2yrs bck Najeeb ya auri Rukayya kanwar Khaleel don tuni suka shirya Kansu da Khaleel kmr bbu abinda ya taba faruwa don tun suna kanana suke tare, duk da ynda dad din khaleel ya so raba su hkn vae yi ba, ynxu abotan gskya suke na tsakanin da Allah hkn yasa Khaleel yyi convincing dad dinsa ya basa Rukayya, Ameesha ma tayi aure abunta suna can waje da Mijinta, Sultan ne ya sauko Downstairs da gudu Sudais na biye da shi a baya, suka nufo Ashfah, sultan ya mika mata hoton hannunsa yana kallonta yace "momy I saw yhu double in this pic" Ashfah ta karba hoton tana kallo ta ga ita da Ashnaah ce ranan wani babban sllh da suka je studio suka dauka, lkci data jikin Ashfah yyi sanyi ta mike xaune a hnkli tace "where did yhu c it?" Yaran suka ce "we saw it in ur room" da kyar tana kkrin mayar da hawayen idonta tace "she is my sister, my twin sister just like both of u re twin" duk suka wara idanuwansu suka ce "then where is she momy? So yhu have twin sis" Ashfah ta share hawayen da ya gangaro mata tace "she is late" duk yaran suka yi shiru suna kallonta, Sudais yace "yhu mean she is dead" Ashfah ta gyada masu kae tana hawaye a hnkli tace "promise me dat yhu will alwayz pray for her in ur daily prayerz everyday" yaran da su ma duk jikinsu yyi sanyi ganin momynsu na kuka suka ce "we promise mum." Duk wnn abinda suke Khaleel na tsaye yana kallonsu lkci daya shi ma jikinsa yyi sanyi ya karaso cikin falon a sanyaye ya karbi hoton daga hannunta ya kamo hannun boyz dinsa yana murmushi yace "promise momy once more dat yhu will alwayz pray for her sister in ur daily prayerz everyday" A hnkli yaran kaman xa su yi kuka suka ce "we promise momy" Khaleel yyi murmushi yana kkrin mayar da hawayen da shi ma ya taru idonsa ya rungume yaran gaba daya har da su Amrah da Afrah, sun kusa minti biyar a jikinsa snn ya ce duk su je sama su yi wasa, suka nufi sama gaba daya ya juya yana kallon Ashfah da ke hawaye har lkcn ya rungumota ya lumshe ido a hnkli yace "I love yhu wife" murmushi tayi hawaye na bin kuncinta tace "I love yhu too" a hnkli ya kuma cewa "Allah ya ji kan fateema, yyi mata rahama, ya sa mu ma mu cika da imani idan lkcn mu yyi, ya hadamu a gidan aljanna gaba daya" Ashfah ta gyada masa kai da kyar hawaye na ci gaba da bin kuncinta a hnkli tace "Ameen" Bayan shekara takwas da rasuwar Fateema Ashnaah mahaifin ta ya gina mata dankareren masallaci da sunanta, Khaleel kuma da taimakon mahaifin sa da gwamnati ya Gina dankareren gidan Marayu da sunan Fateema Ashnaah, Allah ka ji kan duk musulmin da ya riga mu gidan gskya mu kuma kasa mu cika da imani da tsoron ka a xuciyar mu idan lkcn mu ya xo. ALHAMDULILLAH, A nan ni Jiddah M Bello na sauke littafina me suna DR KHALEEL, Allah ya yafe mani kurakuran da nayi a ciki. Na sadaukar ga littafin nn xuwa ga beloved Kanwata Maryam M Bello, nd every odza Maryam round the word, Allah bar mun ke Kanwata me so na da duk kannina ya kuma bar mana uwar mu me son mu Ameen. Allah bar min ke Auntyna Anty Rukky me sona me son ganin na ci gaba momyn Khaleesat smll da Yusuf, Special greetings to yhu my kawalli Maman Shakur for yhur encouragement nd advice from d beginning of dis nvl to d end Allah raya maki kidz din ki Ameen, ina mika sakon gaisuwata xuwa ga Jeedah Aliyu namcyna nd every odza writters masu yi da Khaleesat Haiydar waow i love yhu ol for ur encouragement, My close frnds nd families bn mance da ku ba Allah bar kauna Ameen, Khaleesat Haiydar Novel groups both facebuk nd WhatsApp I greet yhu ol with respect Allah bar xumuncin mu, nd finally my FANZ waow Allah kadae yasan ynda nake ji da ku har cikin raina, Allah bar kauna, Allah sa ku gama da iyayenku lfya Ameen, I greet yhu ol wit respect. Tnx once more. Maman farida tnx also for helping me bring out the necessary point in my Nvl Dr Khaleel, Allah raya maki farida. Nasan mutane da yawa sun fito da points ssae a nvl din, su ma ina gaishesu ssae. Taku har kullum Jiddah M Bello AKA Khaleesat Haiydar. Duk wnda na bata ma ko kuma na taba bata ma ya yafe ni don in mu ne yau ba mu ne gobe ba. Addu'ata a ko da yaushe shine Allah yasa mu cika da imani Ameen. °°°°°°°•••••••••°°°°°°°°°DOCUMENT MADE BY SALMA°°°°°°°°°•••••••••°°°°°°°° adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *