Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, April 3, 2017

fuska biyu cmplt

adsense here [1:27PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: FUSKA BIYU Part 1 NA HALIMA ABDULLAHI K/MASHI Fuska Biyu 1-----1 NA leko a hankali ina sanda bana son mama ta ganni nasan sae tace na saka hijabi, in har kin ganni da hijabi, to ki tabbata islamiya ko sallah, don ko an matsa min nasa dana fita waje zan aiko dashi. Anyi fadan , anyi dukan , an gaji an barni sai addua inji mama. Na kusa kofar fita inajin mama tana fadin "ke! Ke!! Ke!!! Asma'u ai tuni na falla da gudu. Gidansu aminiyata Rahma zan je, ina sonta gashi ta juri zama da halina na masifa da tsokana, duk da ana cewa sai hali yazo daya ake abota, amma ni da Rahma ba haka bane, ita tana da gudun zuciya sam batason fada haka nan ita ma'abociyar sanya hijabi ce, duk kawar danayi sai mun bata, amma banda Rahma. Na kalli gidan dake kallon namu, maza ne zaune a barandar gidan kusan su hudu. Yaya Ali ne da abokansa a raina nace sarakan sa ido , riga da wando ne a jikina na jeans da farar shirt ko ince top, ta dame ni sai dan karamin gyale irin shigar da nakeso kenan a duniyata, kuma a ganina ban wuce wannan shigar ba, tunda yarinya ce ni 'yar sha biyar. zan sha kwana layin su kenan sai gata, nace gidan ku fa zanje Rahma. kefa sai ina ? tayi dariya , nima gidanku zanje . nace to mu koma naku gidan wai ta ce a'a ni fa da shirin islamiya na fito , lokaci nayi sai mu wuce. naja tsaki to zo muje , amma Allah ban so komawa gida yanxun ba , tace saboda me? nace kin san Allah Rahma ban san me na ma yan gidanmu ba , duk sun tsane ni. tace ba tsana ba ce Asma'u , don nasan bai wuce ana miki fadan natsuwa ba. Na harare ta bansan me nayi na rshin natsuwa ba, kina nufin ban da natsuwa ko me? Ganin yanda na hayyako mata yasa tace , "Allah ya baki hakuri Asma'u , ba ina nufin ba ki da nutsuwa bane , kin san....."na katse ta "nidai yi min shiru malama zo muje in zaki. "muka taho sungun-sungun babu mai magana da wani, don ta mantar min da fushina sai tace ina Suraj? nan ko na soma murmushi , nace daxun shine ya dauko ni daga makaranta. hirar suraj muke har gidanmu , ta nufi gurin su mama ni kuma na nufi dakinmu, don na daura zani akan wandona, nasani na nufi mama a haka laifin zai zama biyu sai dai kash! ina isa dakin na samu su yaya yina masu cin ubana Anty Ainau da Anty fati da Anty salima, zan juya Anty salima tace "ke zo nan 'yar iko zo gidan uban wa kikaje a haka? nace "ni ba fa inda naje" na nufi sasansu mama ina yan kunkunai ku kun cika takura gara naje gun mama a haka bata da saurin hannu ku kam yanxun kun duki mutum. na samu Rahma su nata gaisawa da mama ta amshi rezar da mama ke yanke farce tana yanke mata. na shiga na dan rabe mama tace dago ta dube ni tace "yanxun Asma'u ba za ki taba jin magana ba? kin fi son kina yawo haka sai kace arniya? haka kika ga yan uwanki koko haka ki kaga Rahma tana yi? ko Aisha da take kanwar ki ta fiki hankali. na bata rai sannan na ce "to ni me nayi mama? ni ba a sona a gidan nan kowa sai yayi ta min fada" mama tace to sai ki rama mara kunyar banza , ba'a son naki me ake da mara ji? ki canja halinki mana ki gani in ba'a daina miki fada ba, karamarki dake sai shegiyar kafiyar tsiya , tace uban me aka miki zaki tsira min kuka? bansan shigowar yaya usman ba sai dai sai dai rankwashi naji kus a kaina, yace shegiyar yarinya daxun uban wa na ganki da shi a mota ya dauko ki daga makaranta? ya kama kunne na baza ki rabu da dan iskan suraj din nan bako sai kin sha wahala? cikin kuka nace bafa ni bace ya usman, ya kara kai min mari ina wasa dake ne? ban sanki bane kenan? yasa kafa ya shure ni na saka ihun da duk yan gidan suka taru amma abin takaici babu wanda yace yaya usman yayi hakuri, saidai suce ya kara min gara ma su umma da hajiya sunce kece ai rashin jinki yayi yawa Asma'u, ace ayi ta fama da mutum? yi hakuri Usman, yace haba hajiya yarinyan nan ta fita zakka a gidan nan in dai kaji an kawo kara nan gidan to ita ce. dazun fa motor yaron nan suraj na ganta ya dauko ta daga makaranta bayan Alhaji ya hana ta kula shi. mama ta fito tana fadin sai ma an hana ta, ta dubi yayunta mana su aina'u wa taga tana kula samari cikinsu? ina ce tun suna secondary duk wanda yazo gurinsu cewa suke yi je gurin mahaifinsu. amma ita da yake ta sa maza a ranta 'yar kankannuwarta yau ta tsaya da wannan gobe da wannan kai ranar dai naci duka tamkar. ranar dae haka naci duka kamar jaka sannan na nufi dakinmu na kwanta a gadon mu ina kuka. rahmace ta ke ta bani baki har aka kira sallah nata tashi fuskata ta kumbura don kuka , nayi alwala nayi sallah haka ma Rahma, ta nufi dakin mama don shirin islamiya don can ta 'aje kayanta, nima na saka nawa duk gidanmu nice na dinka wando a kayan islamiya(not clear but ana fadin yanuwanta duk dogowar riga suke sawa na islamiya ita ta dinka wando ranar dae duk wanda xae mata fada xaece ta ringa koyo da halin kawarta Rahma har ta ji haushin ta ) ta biyo ta tana kira na ban tsaya ba sae tayo gudu ta same ni , muna fita lungun layinmu ta baya muka bi sannan muka kama hanyar islamiya, kamar daga sama nafa motar suraj na tsaya itama rahma ta tsaya yayi parking ya fito kyakkyyawan yaro dan masu kudi mai takamotoci na kece raini, ya nufo mu baby lafiya? na soma hawaye ya kama hannuna. oh please stop crying my baby Rahma ta dube ni cikin takaicin yanda na tsaya ya rikr min hannu zomuje ka da muyi latti fa asma'u . nace ki tafi sai nazo. tace yanxun nan fa ya usman ya ce ki daina kula samar, na daka mata tsawa ina ruwanki? ta wuce yaja hannuna muka shifa mota ya share min hawaye da yatsanshi, fadamin me aka miki? nace wai ya usman ne yace na daina kula ka hrda dukana, yace to baby ke yanxun yaya kika gani zaki iya rabuwa dani ko ko yaya? ni dai gaskiya baby ba xan iya rabuwa dake ba, nace ai nima suraj ba zan barka ba bayan duk garin nanm kai ne kadai me sona, su fa ba wani sona suke yiba, yace to mujr in kaki makarantar, yace bari mu dauki rahma, nace barta kawai itama yau haushinta nakeji. ina shiga ajinmu duk sauran yan ajin suka gyara xamansu dan bani guri. nice na zabi gurin kuma nace nan ne gurina duk da kasancewa kowa yana zam a ko ina, amma ana shakkar zama wurina , saboda masifata duk da karfi ne dani ba suna tsorona kasancewarbamu taba danbe ba shiyasa suke min kallon karfi. na zauna ina tunanin yanda ba'a sona har zuwa san da rahma tazo. malam ya shigo yana rubutu. ba yabon kai ba, saidai ai min shaidar rashin ji, amma in dai karatu ne daga boko har islamiya nayi zakara. yanda malamai suka sanni da rigima haka suka sanni da kokarin karatu, wannan shi ne yas nake da farin jini cikin dalibai , suke kuma shakkata. hour kofar gidanmu motar ta tsaya, na fito tare da godiya tacemin zai zo anjima nace to sai dai yatsaya daga farkon layin a wurin wani gidan dake duban gidanmu ya Ali ne shi da wani wanda ban tantance shi ba , sai dai ina ganin kila shima dan gidan ne, yana ta min kallo mai kama da harara na wuce ina ce ma wanda ya rago min hanya sa anjima . yaya umar ya dubi kaninshi Aliyu yace, Ali wannan yarinyar yau ganina da ita na uku kenan, tana shiga gidan baba Alhaji itama 'yars ce? aliyu yace Asma'u? 'yarsa ce mana itace mara jin gidan, yace na kula daga zuwana shekaran jiya zuwa yau na lura bata da kamun kai, su Abubakar suka barta ta baci haka? Aliyu yace ai ya uwar yarinyar nan 'yar daru ce da taurin kan tsya. [1:28PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu1-----2 suna iya bakin kokarinsu. ya umar yace 'yar wacece a cikin matan gidan? Aliyu yace, 'yar mama ce ka ko san albasa batayi halin ruwa ba. ya umar yace 'yar mama? Ali yace kana mamaki ko? wallahi 'yarta ce daga ita sai aisha auta, ya umar yace lallai kam albasa bata yo halin ruwa ba, mama da dukkan yayanta salihai ne kai kaf gidan ma babu mai wata matsala shiyasa naje mamaki kaya matsattsu jibi atamfar dake jikinta yanxun tamkar tayi nishi su yage haka suke a jikinta. Aliyu yace kaga kadan ma ba dan tana shan wahala ba ma kila da tsirara xata dinga yawo kuma ga smari kamar hauka yau wancangobe wancan, 'yar karamar yarinya jamilar gidan nan fa ta girme ta . ya uwar yace kai haba? Ali yace wallahi bata wuce 14 ba, ya umar ya mike ya nufi cikin gida yana fadin shi fa ganinshi an barta ne ina zaune bakin gado inayin note shema'u ta shigo "Asma'u ki zo in ji alhaji " na dube tacikin faduwar gaba don nasan kiran babanmu dani babu alkhairi , kila ma an kai mishi karata , na ce to me nayi? tace oho in ce kina zuwa ko ko in ce baza ki zo ba? na harare ta sannan na mike. shi kadai acikin madaidaicin falon nashi yana zaune yana lissafin wasu kudade gefe yaya Abubakar ne da yaya usman, suma suna ta rubutu nasan harkar kasuwancin su ne. na zauna gefe nace gani Alhaji, a tare ya abubakar da ya usman suka jeho min harara sannan suka cigaba da aikn su. Alhajiya ajiye kudin hannunshi gefe yace Asma'u wato kina da kunnan kashi ko? a raina nace tome kuma nayi? yace tambayar ki nake yi?nace a'a yace me yasa ba kya jin duk abin dana gaya miki da wanda 'yan uwanki suke gaya miki? na sun kuyar da kai ya cigaba "na raba ki da yaron nan suraj amma kin ki ji ko? ke ba mashi ba ko wani saurayi na hana kin ki yarda duk yaushe kika tafasa har da zaki kone? wato baza ki dubi yayyanki ba babu wacce take tsayuwa da wani saurayi fa sai da izini na. ma'ana sai an gana dashi sannan na yarje musu kin ga suna tara maza saike? to kiran da na miki yanxun na yanke hukuncin tunda ke ba zaki yi abin da nakeso ba to kema bazan miki wanda kikeso ba . tunda nine na haife ki ba kece ki ka haife ni ba, kuma ni da mahaifiyar ki baza ki sa mana hawan jini ba, don haka na daina biya miki kudin makaranta , na daina miki sutura , ke na daina miki komai ki dai ci abinci sadaka sannan shi wanda na rabaki da shi ki ka ki,sai ki ce masa ya fito, sadaki kawai zai bada a daura muku aure, ki debi yan kayanki ki bishi allura bazan sai miki ba. tashi ki bani guri na soma kuka domin duk iya shegena ina tsananin son makaranta kuma ina karatu sannan nasan ina son suraj amma munyi da shi aure sai na shiga jami'a lokacin shi kuma ya soma aiki tunda yanxun yana A.B. U zaria. (garin su xee lolz) nace don Allah Alhaji ka tamake ni mana? ina son karatu na , yace sanin kina son ya sani kuma zan katse miki shi ba? yaya zan so abin dakike so? alhalin ke da na haifa kina kin wanda ni nake so ? zan kuma magana yaya Abubakar ya daka min tsawa tashi shegiya. dakin mama na zame ina cewa cikin ihu , ki taimaka min mamana don Allah zan mutu tace menene? na ce alhaji ya cire ni daga makaranta wai zai min aure bayan gasu anty Aina'u nan su da suke poly ai sune ma zasu musu aure ba ni ba, na tsaya ina ta rusa kuka, ta ce hakan ne ya dace da ke tunda ba kya jin magana Asma'u duk kin bi kin maida kanki 'yar iska kin zubar mana da mutunci a gari? da gudu na nufi dakin umma suna zaune da anty fatima na fada kan umma na ce umma ki min rai mana Alhaji yace ya cire ni daga makaranta ku roke shi na tuba ba zan kuma yin komai ba, tace so naea zaki ce kin tuba amma ai tuban muzuru? tunda kin ja yayi fushi dake ba shi kenan ba. jin ba sa'a na nufi hajiya gara ita tadan lallashe ni tare da bani baki kuma tace mu bari ya huce sannan naje na roke shi tare da daukar alkawarin daina halayena, kai ranar naga tsawon dareban fasa ba haka nan ban karya ba bare na nemi kudin mota, hasalima a sace na fito tun daga sabon kawo har F.G.C malali a kafa san da na isa har an tashi break sai dana yi hawaye don takaicin missing din darasi har. 3 yanda muke shirin fara. test dinnan. haka da muka tashi bayan da Rahma ba tayi ba akan na zo muyi goyo a mashine amma naki, haka nan ta hakura ta tafi su shema'u da hadiza da Aisha suka hau mashin a gabana hakan ya kara sani yanke hukunci bani da mai kaunata duk gidanmu. na iso badarawa na gaji sosa na samu guri na zauna hutawa nake yi can kamar daga sama sai ga suraj cikin mota , ya fito yazo har gabana ina kallon shi ban ko matsa ba , yace nasha yawon nemanki baby tun daxun naga Rahma ta sanar dani kina tahowa a kafa kuma a kafa kika je makaranta . nace meyasa tace baki fada mata ba, na dube shi duk kan ka ne suraj, baba yace saidai ka fito muyi aure na gama makaranta ba zai kara biya mun ba, yayi shiru bayan ya tsugunna kusa dani, yace to yanxun yaya zamuyi? nace shine ban sani ba, yace yanzun dai taso muje na ce, a'a yaya zan shiga motar ka? a kuma ganina? yace sai na sauke ki bayan layinku , na mike na shiga a hankali muke tafiya, tare da neman mafita a karshe muka yanke shawarar zamu na haduwa a bayan layinmu kuma ba zai dinga zuwa da mota ba kuma yace ko ma nake so na tambaye shi zai na tambaye shi zai min yace ma zai saya min waya sai na boye ta mu dinga magana, son da na shiga gida ana sallar la'asar ban kula kowa b ni a dole ba'a sona na daina kula kowa haka na yanke shawara nayo alwala nayi sallah nasa kayan islamiya Aisha ta shigo. Asma'u kizo inji mama, na nufi dakin na shiga a raina nace nasan dai laifi nayi tunda dama nice uwar 'yan laifi mama ta dube ni ga abinci nan a kicin tun da yake ke kn fi karfin ki manamagana 'yar gaisuwar da kike mana a raine yau bamu samu ba, idona ya ciko da hawaye na ce na koshi , tace to ai shi kenan kila mai hure miki kunnan ya baki wanda yafi namu an hana ki zuwa makaranta amma don ki nuna ma duniya cewa bamu isa. ba kin tafi, na soma sharar da hawaye cikin shessheka na ce mama na ga ne term bai kare ba kar ayi asarar kudin mama tace ina ruwanki , me biyan yace ki daina zuwa ko sai yaje har makarantar yasa an goge sunanki zaki daina zuwa? ba tare da na sake wata magana ba, na mike na nufi dakinmu , na cire hijabin na kwanta kan gado ina mai tausayin kaina tare da tunanin anya kuwa gidannan ba tsinto ni suka yi ba? banyi tsammanin haihuwata akayi yi ba,kila ni ba 'yar asalin cikin gidan nan ba ce. nayi kuka har na gaji ga yunwa amma nasan ko na tasa abincin ba zan iya ci ba, naji an zauna kusa dani an dafa ni ko da ban juyo ba nasan cewa Rahma ce . na dago na dube ta tace "Asma'u me ya hana ki xuwa islamiya? nace cikin kuka an cireni da sauri tace an cire ki? nce har boko ma, saboda me? nayi shiru ta kana ni tashi ki gayamin nasan zaki dan ji sauki in kin gaya min kila ma mu samu mafita jin haka na tashi zaune na koro mata komai tayi shiru na dan lokaci sannan tace Asma'u xan gaya miki gaskiya, duk laifn ki ne menene wuya cikin yi kaza bar kaza? duk shine ya janyo wadannan matsalolin nace ni yanxun yaaya xanyi tace ki bar makaranta a kaman kwana 3 sannan kije ki ba alhaji hakuri ki gaya mishi kin daina kuma ki rabu da suraj.sai dai bazan boye miki komai ba rahma, ba zan iya rabuwa da suraj ba, tayi shiru cn tce to sai ki cemasa ya dan daina zuwa tukunna nace saidai hkan, can tace Asma'u zan tambaye ki, donAllah wani abu. bay kuw shiga tsakaninki da suraj dinnan? [1:29PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu1------3 na dube ta kamar yaya? ta dan yi shiru sannan tace, kiyi hakuri yanda naga yake rike ki sai ina ganin wata rana zai iya neman ya sanki matsayin ki na 'ya mace , na ce Rahma mutane da yawa suna min wannan kallon amma ba haka ba ne, yan layin nan ma 'yar iska wasu suke ce min, niko ba haka nake ba har yan gidan nan kallon da suke min kenan . a layin nan. ma na lokacin da nayi ciwon nan? tace eh nace akwamasu cewa an cire min ciki ne. rahma tace saboda irin shigar da kike yi ne Asma'u , ki daina an fa taba takawa ba so daya ba ba biyu ba, aka ce momynah ta rabani da ke , ke 'yariska yarinya ce, momy tace Allah ya shirya ita ba ruwanta, nace duk masu min sharri su da Allah . rahma ta ce kema ki kiyayye abin da za'a zarge ki , nace ni raba ni da gulmar mutane yanxun me zai wanke ni daga zargi sai Allah . yau kwana na takwas rabona da makaranta na fito zanje kitso jikina riga da skirt material ya dme ni tmkar zasu yage,in nyi kwakkwaran nishi duk kayan haka suke don an mana dinki zan dauki nawa in je a rage su, ya uwr ne yana kokarin hawa mashin jikinshi d kaki sojoji, wata randneniyr mashin ce ban taba ganin irin ta ba ya galla min harara nan take nima na rama a raina nace don kana soja zanji tsoranka? na tsallaka dayan gefen da gudu ya kwaso mashin din ya bi ta ciki wani ruwan tabo duk ya fancale ni da ruwan da karfi nace Allah ya isa ashe yaji , nan ya dawo ya dauke min fuska da mari tare da fadin 'yariska mara kunya. na dauki alwashin sai na rama , ai wannan cin zali ne. ga bata jiki ga duka? daga nan ban kuma ganin shi ba har sati biyu , sai wata rana suraj ya dauke ni mun tafi shan ice cream a gamji , dama unguwan dosa muka hadu ya daukeni saboda yanxun baya zuwa layinmu yana ma makarantar shi , sai weekend yake zuwa , snye nake da riga da wando na jeans yana rike da hannuna muna tafiya muna hira ina zaton ramar sojoji sunyi wni taro anan wani hall dake nan gamjin , sai hangen ya umar naayi ya tsaya yana kallonmu, daidai lokacin suraj ya tallabo nii zuwa gefen kirjin shi ya girgiza kai ya wuce nace suraj zo mu tafi wancan mutumin yaron abokin Alhaji ne kuma layinmu daya ka da yaje ya fada nan muka dawo a raina na tsani ya umar, ban ma dade ni da sanin shi ba wai ashe tun yana karaminshi yake karatun soja tun bayan da yagama primary, yayi karatun soja sosai yanxun yana aiki ne a port harcourt , wani course yazo kd yana jaji shi ne ya kanzo gida. Alhaji Ahmad shine mahaifinmu mijin mata 3 mama itace uwar gida kuma auren zumunci. su 'yan asalin gombe ne , fulani ynxun haka dangin su suna can kasuwancin ne ya kawo shi nan in da yake saida zannuwa , atamfofi , laces, shaddodi, da sauransu . a yanxun shagunan sa 3 cikin central market . mama tana da yara 8, yaya abubakar, ya usman , ya mas'ud, yaya sani, anty aina'u , anty fatima, sai ni is auta Aisha, ita ko umma 'yar kano ce kuma a can ya auro ta duk dai gurin harkokin kasuwanci suka hadu 'ya'yanta 3 shema'u sai hadiza sai hamza, shema'u sa'a ta ce ta dan girme ni amma kadan, hadiza ce babba. ita ko hajiya A'I makka suka hdu , ance auranta 4 bata haihuwa ba sai data auri Alhajinmu , tashin farko ta haifi yan biyu hassan da usaina , yanzun tana goyon gambon su . yanzun tana goyon gambon su , Ahmad sunan Alhajinmu muna ce masa khalifa. mama mace ce mai tsananin son zamn lafiya , na yarda mace ta gari ita ce sila ta zaman lfy , domin duk yanda mutum yaso ta shin hankali ba zai yi da mama ba, tana da tsananin gudun bacin zuciya , tare da ibada ga biyayya ga miji ga kuma tarbiya mai ban sha'awa da take ba 'ya'yanta wannan yasa kishiyoyinta suke girmamata tare da sakar mata duk wata shawara ko 'ya'yansu suna matukar son mama. Ya abubakar da ya usman babu nisa tsakanin su , don haka tare suka shiga makaranta tun daga primary har zuwa jami'a , sunkaranta degree dukkansu fanni kasuwanci da suka gama basu nemi aiki ba sai suka fada kasuwanci gurin Alhaji inda ya bude musu wani tafkeken store kayan kwalama dana shafe shafe zuwa suturu akan titin isa kata dke unguwar sarki , yaya mas'ud da yaya sani yanxun suna b u k , Anty aina'u da anty fatima suna poly, hadiza tana ss1 fgc malali, shema'u js3 Aisha primary 5 hamza da yan biyu suna pri 1.ba yanda xaka gane wannan dan wannan ne babu bambamci koh 'yan ubanci, ni kadai ce matslar gidanmu, kamar yanda suke cewa na fita zakka, ni dai tunda na taso nafi son wando fiye da zani ana sai min wanduna amma dana soma tasowa mama ta hana sai dai siket in ko aka dink min zani sai naki daurawa insa riga in ta yawon daga ni sai pant sa rig, wannan yasa ake dinka min siket da na kara wyao in an dinka min sai na kai nace yayi yawa wai a rage, gani tubakallah yarinya ce ni amma ina da diri mai kyau kuma kafatanin gidan mu farare ne yaran gidan nice baka, sai dai naji ana cewa duk nafisu kyau. tun ina js1 maza suke sona wannan yasa na soma tunanin ko dn nfi 'yan gidanmu iya ado ne, d nuna jki su anty aina'u basa tsayawa da samari har suka gama secondary skul, sai yanxu kuma gurin alhaji suke turo duk wanda yace yana son su kamar yanda mama take ce mana duk wanda yace yana sonmu to mu turo shi gurin Alhaji su take gaya ma don tace ba'a zo kanmu ba yanxun haka duk suna da wadanda zasu aura Anty aina munnir dan sokoto ne yana aiki ne a nnpc kd, is anty fatima , Aminu yana nafdac lagos , hadiza dai ina ganin Aliyun gidn Abba zata aura naga yana dan kiranta. Abba Aminin alhaji ne dan sun wuce abokai. abba dan bauchi ne mutumin azare , kuma tun a gombe suke abotarsu , har yau. Abba shine silar zuwan alhaji kd. Abbba yayi karatun boko mai zurfi kuma ma'aikaci ne bai dade da yin ritaya ba, saboda abota ne suka yi gidanjansu layi daya sabanin d abba 'yan unguwar sarki . Alhaji yana unguwar dosa sunan Abba Alhaji muktar , yana da mata 2 uwargida momy kawar mama ce kut da kut , babban yaronta soja ne umar yana port ya girmi yaya abubakaar din gidin mu sai aliyu dan bata haihuwa da wuri tsakanin umar da aliyu shekara 9 , Aliyu ma'aikaci ne. bnkin phb sai anti salima zak zata yar mamace saboda kusn ma a gidanmu take, sai nafisa sa'ata sai yan biyunta hassan da usaini, na manta da jamila daga itace sai nafisan jamila ce sa'ata koma nace kawata mama ce tace ta daina bina kar na bata ta , mamanmu [1:30PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu1------4 Ya umar tunda mugu ne yanda naji su anty salima dasu anty aina suna lbr tun suna kanana, ysha basu wahala musamman inkn ci na 5 a makaranta zuwa sama, amma daga na 1 zuwa na hudu yana maka uzri inko kaci sama da haka ayya sunan ka sorry, zai zane ka tas ya saka ka kallon rana irin da mugancin su na sojoji. wata rana su anty fatma da anty aina sunjehutu gidan shi ma yazo hutun, ayya sun sha wuya , yana zaune a falo yana kallon kwallo. suma suka zauna yace bakun zaunaba saura naji surutu, dama ina ciki daku suka yi tsit suna ta kallon kwallo anty fatima tace ni dai nafi son masu fararen kaya su ko anty salima da anty aina'u suka ce sunfi son jajayen, ashe shima yafison fararen wato asnal.can jajayen suka ci, hu suka soma fatima sun ma manta da batun yaya umar yana ciki, haushi 2 ya kama shi ga haushin anci garin shi ga ihun su, nan ya had kan anty salima da anty aina'u ya gwara sannan yasa ka su zaman mashin da tsallan kwado sun yini suka kuka dan sun gaji a karshe ya musu bulala 20. ni kuma in sun bani lbrn shi sai ince ce ya rana ku ne ina ma lokcin ne da sai na nuna mishi nawa taurin kan, anty aina'u tace ai da yanxun ne shi ne maganin shegen taurin kanki in ce sai dai mu zuna shine yanzun ya soma nunamin? y jika ni sannan ya mre ni? zan rama. yau kusan watana dy da daina zuwa makarant kullum cikin roko nake har anyi jarabawa bana nan , ranar ko anyi kukan d dukmai sona sai ya tausaya min amma 'yan gidanmu ko a jikinsu. Alhji ma da mishi maganar yayi hakuri na daina sai yace ai ban rabu da suraj ba, saboda haka sai dai in suraj din ya fito ayi auran can naci gaba da karatun gidansu. na shirya zanje gidansu rahma kuma inason ganin suraj dan in san yanda zamuyi, tun daga abin da alhaji yace , cikin sa'a ina ftowa sai naga mugunnan ya umar, suna magana shi da wani abokinshi ne ko yaya suke oho, duk suna sanye da kaki, na koma cikin gda hadiza tana wanke wanke kwanuka, na suro an sannan nazo na antayamishi tsayawa sukayi suna kallona, nace kima kaji inda dadi, ya Aliyu kaninshi dake can bakn gate din su ya taho da sauri yana fadin ke karamar mara kunya shi tsaronki ne? nace ehdin kai kuma ina ruwanka?zai kai min mari ya umar ya rike shi yace barni da ita kada kayi fada da karuwa....mutuncin ka zai zuba na san maganin ta , kinga yanda kika jika kakin nan sai kin wanke su, so dari nace ba so dubu ba? ai sai ka sani na wanke, ya ce ayya ai baza ki iya ganewa bane , sai randa ki ka fara mara kunya , karamar karuwa , kalmar da tamin zafi kenan na kara tsanan shi, wai ni ce karuwa nace eh to karuwar ce naga dai ba jikin wani bane koh? na koma gid cikin takaici , abokinshi yace amma aminina yarinyar nan bata da kuny , yace barta zata gane kurarta,kasan mata ba abin fadan soja bane, zan azabtar da ita ta manta hanya. a daren ranar muna tare da suraj ya bani waya kirar kamfanin samsung yar mai kyau da layinta duk gidanmu su ya abubakar ne ke da waya sai alhaji sai ko landline da ke falon kowacce matar gidan boyeta nakeyi cikin wando suraj sai ya kirani musha hira inba kowa a dakin. gaskiya inason karatu na , don haka na matsa ma suraj inaso mu gana, muna cikin motar shi ya dube ni menene kike son ganina baby duk ya kosa menene kike son ganina baby duk na kosa dare yayi danna amsa kirar gimbiya? mata na dan hada rai yace bakiyi kyau ba,ya juyo da fuskata gayamini mana sweetynah, nace nifa na gaji da sauri yace dame? nace da zama babu karatu ba zan boye maka ba tunda alhaji yace ka fito, to ka turo kawai ayi auran in yaso sai naci gaba a gidanka , tunda yanxun yaki, 'yan gulma suna gaya mishi muna tare. yayi shiru na lokaci can yace kin san yanda muka yi ta kai ruwa rana dasu daddyna kuwa? ban gaya miki bane saboda banason hankalin ki ya tashi sun dage kan cewa ban isa aure ba wai 21yrs me zance ma matar? kinji fa yanda nake jina garau ko 4 suka zuba mini. ai zasu sha mamaki , nace ni dai yanxun ba wannan ba mafita nake nema, tunda nima ai da saurana , auran dan dai rashin gata ne yasa za'a min yace. to ko in canza miki makaranta? na a'a wai raba ni ai kilama sai su mama sun tsine min duk mukayi shiru , a ranar dai har kusa 10:30 babu mafita kafin daga karshe mukayi sallama akan kowanne zaiyi tunani Abba ya daga kofin shayi yana sha kuma gefenshi anty ce amaryar shi yace kiramin hajiya ta mike ta nufi dakin hajiya anty haka yaran gidan suke kiranta bata taba haihuwa ba tana matukar son 'yakyan mijinta dayake ance mai da wawa na ne yasa suke matukar zaman lfy da momy hakan nan ya umar dan dakinta ne yanxun nan zakaji suna hada plan akan wani abun in ba'a son Abba yayi fada bayan sun dawo sun zauna , abba yace hajiya Aisha kin san dalilin kiranki? tace a'a yace na gaji da zaman umar haka, na bashi dama ta farko na bashi na biyu , na kuma nashi na uku wannn karon na gaji xan nemar mishi mata. momy tace gara haka ni kaina nayi nayi yaki saurarena amma ga anty tashi nan ina ga ita ce zata fini sanin meke faruwa? tunda itace abokiyar shawarshi yayi murmushi ya dubi anty tasu yace to ke anty su yaya kuke ciki da dan gidan naki? ya zama tuzuru anyi karatun anyi course din har so nawa am kuma aiki sai me? momy tace sai aure, anty tace kada ku damu, yarinyar da muke so ce tana kartu da a son ranmy sai in ta gama ya zama daidai da mun kammala gininmu Abba yace a'a wannan katafaran gidan na umar ya mishi kadan? anty tace ba nufin mu kenan ba, abba yace to ku sake shawara na baku wata 2 in lokacin ya cika babu wani bayani zakuji nawa bayanin maganar yarinya tana karatu ba ayi da aure ne? momy tace yi kai yace to. donhaka wannn cekarshen magna, anty tayi dariya tace munji abb insha Allah zakaji mu kafin lokacin dakaba mu . Na samu da kyar da taimakon hajiya da umma Alhaji ya yarda na koma makaranta bayannasha tsauraran dokoki nace wa bani ba suraj ,bani ba kananan kaya sannan in daina tsiwa na yarda duka zan bari amma banga zan iya ba, na koma makaranta cike da murna da farinciki.surajkam muna tare sai dai a waya, waya cikin sirri na rage saka wanduna sai dai riga da siket suma din damammun ne sai dai yan dan fi wandon haka yasa wasu sakar min fuska ganin su na shiryu. ya kishin gida bayan ya aje kofin gilashin da ya gama shan juice yanxu ya ciro wayarshi ya soma neman antynshi ringing na 2 ta daga yace Allah ya bar min antynah ya gidan? tace lfy ba lau ba , ya gyara zama me ke faruwa a gidan? tace abba ya bamu lokaci yace wata 2 in mun wuce haka za'a mana auren dole , ya saka dariya auren dole anty ai na wuce nan, ta sak. dariya da gaske Abba keyi har momy fa, yace ai momy ita ce ta zuga shi anty tace menene lbrn farida saboda gara asan nayi fa? yace tun wancan satin muna tare babanta ne matsalar yace bai yarda tsarin ana aure ana karati ba, ni kuma gaskiya inason yarinyar sai kinganta antyna , tana da kyau ga ilimi ga hankali, ga kamun kai samun kamar farida sai an tona Anty tace guri yayi nisa ne shiyasa ban ganta ba , yace hakane amma kinsan yanda zamuyi? tace a'a zan kirata a way,inji in har tana nan port din zanje mu ga yarda za'ayi Anty tace ya kamata ka sani ne? yace a'a tace kace manyanka zasu zo in yaso in sai a saka lokaci zuwa sanda zata gama makaranta yace kin kawo shawara antyna saidai nazo karshen wata suka ajiye waya tare da fatan alkhairi ga juna ina cikin saba sabulu naji wayata dake gefe ta soma ringing nayi sauri daukar zanina na goge hannuna jikina kam duk kumfa na daga wayar ina tsoron kar wani ya jiyo ni , nace suraj yaya ne? yace zakije party dinne? nace wanne kuma? yace na faisal kin manta ne? nace oh birthday din faisal kake magana? yace eh, zanje mana yace yauwa har naji dadi saboda kinsan in an tashi daga na gidan su akwai wanda muka shirya mishi iyaka mu friends da beb dinmu, a maharaja hotel nace duk a yau? yace eh na gidansu xa'ayi 3 zuwa 6 mu kuma 8 zuwa yanda ya samu nace zanje is dai kasan yanzu an samin takunkumin yawo kuma an amshe min wanduna na yace dan wannan karki damu zan sai miki wasu in mun hadu sai ki saka nace to zan san yarda zanyi in fito ko ban samu zuwa na gidan su ba sai muje chasun , yace haka ne tawn me kike yi ne yanzu? nace wanka fa nakeyi yayi driya kiyi da kyau babynah , nace take care, da sauri na karasa wankan na fito ina shafa mai ina tunanin irin karyar da zan sheka dan na samu fita da dare, gani da son party. [1:31PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu1-----5 Gani da son party rawa dama sai kace indiya ta haifi ni, ranar dai na rasa mafit hour magrib, can dabara ta fadomin na samu mama a daki nace mama zanje in gaida momyn su rahma bata da lfy , ta dube ni zani da riga na saka ga wani zumbulelen hijabi na shema'u ne ma nasaka fuskarta ta nunamin taji ddin hak , sannan tace ki gaida ta nim zanje na dubata , nace to ina fitowa suraj na min waya, na dauka yace kin samu fitowa kuwa? nace eh ynxun na fito amma zanje gidan su rahma kasan da ita nayi karya, yace to in kin fito gidan su ki same ni a karshen titin laynsu nace to, mun gaisa da momy sannan naje gun rahma mun dan taba hour inda ta nunamin jin dadint da ganin shigar da nayi cewarta wai na fi kyau, nace zan tafi tace da sauri haka? nace ina note ne fa kika fadomin a raina naji ina son ganinki shi ne akace kar in dade, kin san an samin takunkumi, tayi dariya sannan tace bagashi ba ana ganin cin nasara? nace haka ne zan tafi in kinzo gidanmu mama tace ya jikin momy , kice da suki tace naje na ma momy sallama ta rakani ni hanya Ta rakani hanya nace ta barni nan tace to mukayi sallama na sameshi yana jirana cikin nota na shiga sai gidansu yau ce rana ta farko dana taba zuwa gidan su suraj dake badarawa. tangamemen gida mai matukar kyau, gefenshi daban ne yace bari muje ta can kusa da dakina kada a ganmu nace to na rude da kayan da suraj ya sai min, kaya ne hadaddun babies duk kala hudu ne amma babu riga dake da hannun arziki , wata ma iya cibiyata, ya soma cire min hijabi yana fadin gwada mu ga wadda zatafi yi miki kyau, kin san zanfi so ki fi bebs din gurin kyau, nace nima zanso haka na kwashi kayan nace bari na shiga nan in na saka sai nazo in nuna maka ko? yace in kinfi son haka shikenan amma inkn gwada a gabana cinye ki zanyi? nace a'a bana son kallo ne. (kawata ta birgeni) duk sun min kyau amma suraj yace na saka wanda tafi matse ni , tun da shi rigarshi tana da hannu daya kuma yafi son rigar nace suraj duba fa cibina a waje haka duk kirjina a waje yake yace ai shi ne hadewar nan na yarda nace gashi ba takalmi d kayan makeup yace karki damu bari na sato miki na mom dina kiyi makeup din Takalmi da jaka in mun fita sai mubi ta wani store din ki zaba, ya fita da sauri sai gashi dasu munata dariya , nace amma ka iya sata naga kana fita har ka sato, yace ai tana dakin dad shiyasa, na taje gashina yayi kyau na kama na dubi madubi nayi kyau matuka saidai nayi kama da 'yan iska (Allah ya shirya) haka nace ma suraj yayi ta mun dariya yace in anyi auranmu kayan da zan dinga saka mishi kenan yana gani nace na yarda kai tun a cikin akwatuna kada kasa atamfa ko leshi zaka zuba, yayi dariya yace kinga munzo da sabon salo kenan ko? nace za dai musha surutu ne, yace ayi tayi muka fito ya canja mota glass dinta mai duhu ce 'yar kucila toyota ce, muka fita sky store muka shiga na zabi wasu shegun takalmi masu tsawo da jaka bakake nan na kara fitowa na zabi sarka da dan kunne fashion na yan gayu sannan muka dauki hanya San da mukaje guri yayi guri zuwan mu sai ihu ga bigboy ya iso haka abokanshi suke kiranshi, nan fa naga bebs 'ya'yan masu kudi sai dai nasan duk da sunfi mu kudi ba mai nuna min kudi da body, da iya ado.don haka nima sai naji kaina yayi sama ai nima wata ce kuma suraj din suna da kudi fiye da suran ashe ma shine shuganan hada partyn. don haka sai na shiga duban su da dai bayan kyar gabatarwa da dan abin da ba'a rasa ba sai aka shga casu, nan fa da yawa 'yanmata suka sallama min samban san dare yayi ba ashe sha biyu, kuma na soma tsorata da yanda naga wasu yarinya da saurayi anyi cikin wani daki, suna manne da juna. kuma a dakin dundum da duhu duk sai na tsargu don ni iskancina bai kai nan ba, don hka sai nace suraj zan tafi gida, yace ki dan bari mana dare gurin ya gauraye da duhu an kashe wuta. suraj ya rungume ni babyna nefa sun dauke wuta, nace muje ka kaini gida don Allah kasan fa da wayo na fito, kmin na karasa sai naji hannu a kirjina da saur nace menene haka suraj? na bige hannun sai nake jin nishin mutanan gurn wani gurnanina fahimci wato masha'a akeyi Nan na soma laluban hanya, suraj yana rike dani nace sake ni tafiya xanyi nan ya soma min korafin banason shi, shi yasa banason yana tabani nace wace irin tabawa ce baka yi min suraj? sa rai fa nason Allah ya hana amma saboda son da nake maka da kuma yanda banason bacin ranka na barka kana tabani na fit waje kafin na fitan ma sai karo akeyi da mutane. suraj ya biyo ni yana ta faman bani bak ya sha gabana ya rike min hannuwa, lallashina yakeyi har da hawayenshi wai yana cikin wani hali in taimaka mashi nace gaskiya suraj ba zanyi zina ba, na kwace hannuna na tafi , ya tsaya yana kallona, can yace baby in nayi da wata baza ki damu ba? ko juyowa banyi ba bare in bashi amsa gabana ke mugun faduwa ganin hanya shiru, lallai dare yayi na ciro wayata ina duba lokaci 12:30 na dafa kirji nace na shiga 3 ! na kara sauri titi na mika babu kowa sai motocin dake wucewa jifa jifa. Wata mota ta tsaya da sauri na isa gurin dan neman taimako samari ne guda 2 a ciki suna shan sauti na bayanne yace shigo mana baby nace taimako nake so sabon kawo zanje , suka ce shigo mun kai badarawa sunata min surutan banza, hardai na bayan ya soma dagamin kafada tare da fadin baby ko zamuje mu dan huta na awa 2 kacl ni awa 1 abokina awa1 ? na dube su cikin takaici nace, ni ni ba 'yariska bace da zaka ce muje a huta , sai naga sun hada ido sun kwashe da dariya. direban ya ce haba yarinya duk wanda ya dube ki yaga cikakkiyar karuwa sai dai in zaki mana rowa takaci ya kamani nace kune dai yan iska bani ba, suka ja suka tsaya ke 'yar bariki kada ki gaya mana magana, sauka nace sai me in an saukan na fita suka ja motor nace 'yan iska kawai. Tafiya nake har ma bansan gurin da nake jefa kafa ba, sai jin taka birki nayi quuu a bayana kan in kauce har motar ta bangaje ni sai gani a kasa, fitilar motar ta dallare ilahirin gurin da haske, ban tashi dga kasan ba naji taku tafiyar mai motor tsoro ne ya kamani a raina nace kilama dan yankan kai ne, takalmin shi na fara kallo gabana ya fadi na dubi wandon soja ne , na fada a raina shi kenan zai kasheni da duka, yce ke na dube shi da sauri saboda muryanshi dana ji gabana yayi mummunar fadywa na'am na ambata ya umar jikina ya soma bari yace ke me sunanki ma? nayi shiru ya dakamin tsawa ya sunan ki nace? nace asma'u , yace tashi da tsawa yakemin magana na tashi yana dubana tamkat yaga kashi cike da tsana yace lallai yarinyar nan kin fita daga sahun kananan karuwai kin koma cikin manyansu, lallai an jibga asarar haihuwa wannan ai gwara barinki da haihuwarki, amma bakiyi halin mama da alhaji ba kai kaf gidanku kece fitinanniya banma san sanda aka haifeki ba, amma har kin kware da bin maza yaja tsaki tare da tsirtar. da miyau ya wuce ya shiga motar shi Hakika naji zafin zagin da ya umar ya min, amma hakan bai hana ni yin saurin zuwa kusa da kofar motarshi nace ka taimaka min ya umar don Allah gida zani ya mini wani kallo sannan yace god for bid in dauki najasa cikin motta? bani ba ban kasance mazinaci ba ba zan dauki mazinaciya ba ya tada motarshi tare da fadin ba kwanan gida zaki je ba? dan rashin imani irin na soja haka ya uwar ya tafi ya barni . ina tafe ina kukan bakin cikin zuwana gurin partn nan nayi nisa da tafya naji wata motar na kauce kar a buge ni, ashe suraj ne haushinshi ya kama ni ya tsaya yana baby zo muje in kai ki gida nayi mishi banza naci gaba da tafiya, yayi parking ya fito haba baby yi hakuri nima sai daga na gane ban kyauta ba, na tsaya danaji haka ya iso zo muje nace kaje kayi da wata dinne? yace iye, a'a haba dai ya shiga 'yan kame-kame naje na shiga motor na ce dubi time suraj kai baka damu ba ko kashe ni za'ayi kashe yi ko? yace a haba yanzun dai ya zamu yi? nace ina kayana , yace gasu can gidanmu, can muka wuce na can za sannan ya kuma dauko ni har maigidansu Har maigadinsu yana ce mishi surajo ina zaka da dare nan yace yana zuwa. tun kafin mu kai gidnmu muke ta neman mafita a karshe ya kaini wani kemin aka dan sa min bandeji a ciwon da naji na kafa sakamakon bigeni da ya umar yayi sai ya kaini gidan wata kawar mama dake rafin guza yace wai ya buge ni ne shi ne na suma to ban farfado ba da wuri sai yanxun shi ne yace ina ne gdanmu na ce rafin guza , na nuna mishi nan gidan nayi shiru na sunkuyar da kai ina mamakin yanda suraj yake tsaro karya . hajiya rabi ta kama dama ta mijinta ya rasu daga ita sai 'ya'yanta shi yasa nace ya kaini can, ka bugu biyu zuwa na uku ta bude gnina yasa ta shiga rafka salati tare da tambayar ko lfy? kafin nayi magana suraj yace ko kin san wannan yarinyar? tace kwarai 'yata ce nan ya shga koro mata karya ta hau kai ta zauna musamman da ya nuna mata plaster kafata . ta shiga gero mishi godiya sannan ta jani cikin gida, kafin na kwanta sai da hajiya rabi tadafa ruwan zfi a kettle ta gasa min kafar da nake ta dingishin karya , nayo wnkasannan Nayo wanka sannan ta tambaye ni yanda abin ya faru, nan na karkacr na sharaara mata karya da cewa ina tafiya n dwo gidan kawata kawai sai naji taka birki ko kafin in ankare har motar ta bugeni, daga nan ban kuma sanin komaiba sai a kemis ni fa ma bansan sanda nace mas a rafin guza gidanmu yake ba, sai da naga mun shigo unguwar sai kuma Allah yasa na nagane nan gidan barka da arziki hajiya rabi ke ta yi min. kafa 'yar albarka dana dinga liliyata cikin dare don ta kumbura kan safe har ta tashi gurin ciwon yayi fushi ya kumbura , don haka nayi murna sosai sanda muka isa gidanmu tuni hankular 'yan gidanmu ya gama tashi banda maama wacce ta ce yawon iskancina na tafi, har umma da hajiya suna cewa ta bar cewa haka yanxun duniya ta lalace. bayan an gama karade unguwa da nemana sai gamu mun iso ina ta dingishi . hajiya rabi tana min sannu.'yan gidanmu suka biyo mu dakin mama suna tambayar meya faru? na yarda da haj. rabi in dai gurin bada kanu ne, domin yand take rattafo zancan babu mahalukin da zi ce ba' gabanta abin ya faru ba, [1:33PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu1----6 Su anty aina'u da umma da hajiya sun tausya min sabanin mama wacce tace ita wannan zncen bai shige ta ba, na dai tafi yawon iskancina ne. jin hakan yasa naa fashe da kuka tare da rantse rantse cewa mota ce ta buge ni, umma tace haba mama yarinyar tsautsayi ya same ta, mma kice haka? hajiya rabi kuma mikewa tayi tana fadin ni kinga tafiyata don na kula bamma miki gwaninta ba . mama tace haj.rabi ba nufina kenan ba , nagode hajiya rabi tace dama tun jiyan take min kukan tasan kila ace karya ne. hajiyan gidanmu tace wani irin karya? nan dai mama tayi shiru ba don ta yarda ba sai don ganin babu wanda ya goya mata baya. haka makota suka yi ta zuwa jaje amma da yawa gulma ce ta kawo su, lbrn ma sa canza shi akeyi har da masu cewa an sace ni ne, dayawa dai sunce party naje yan sanda suka kawo hari gurin gudu mota ta bige ni, nace kowa dai yayi ya gama ni dai dama Alhajinmu nafi ji kuma tunda ya yarda har da kaini asibiti a duba ni ko na bugu a wurin gurin mama ko haushin maganar takeji domin ta hakikance karya ne. Momy da anty suka gaisa da mama tare da mata jajen kade ni, tsaki mama taja sannan tace kema hajiya aisha kin yarda? wannan zancen karya ne momy tace haba ke ko maman su aina'u me yasa zaki dinga biye ma surutun 'yan unguwa? duk da rashin jin asma'u ai ba zata prtyn dare ba, dn 'yarki ta samu hatsri shi kenan ki bita da mugun zargi, anty tace Allah ya shirya mana, mama ko cewa tayi dama aike tuni baki son laifin asma'u hajiya Aisha momy tace ai ni 'yar gidana ce duk cikin yaranki babu wacce nakeso kamarta. mama ta ce lailla don ba zaune kuke guri guda da ita ba, sun fito mama ta dan tako musu suka tafi gida suna shirin shiga ne anty tace momy ga motar dan gidana yaushe ya shigo kd? mama ta dubeshi yana kokarin parking tace kila ma nan ya kwana ya karaso cike da fara'a yana fdin daga ina ku ke? momy ce ta soma cewa Allah sarki yarinyar nan ce 'yar gidan hajiya saude tsautsayi ya same ta, yace 'yar gidan mama? tace eh yace aina'u ko fatima? anty ta amshe da cewa asma'u din nan, itace wai mota ta kade ta ta suma har ta kwana gidan wata kawar mama din Mamaki ya cik shi yace yaushe? momy tace shekaran jiya da dare, zuwa gidan kawarta gada maman kawar an ce bata ma dade ba a gidan su rahman tsautsayi ya fito da ita tun kilama akan layin ne motar ta kade ta har karfe dayan dare bata farfado ba, ya umar yayi tsaki sannan yace wannan 'yar iskar yarinyar ba wata mota yawonta.... momy ta katse shi to sarkn zargi kai da ba ma anan kake ba na kasan tana yawon taja tsaki ta nufi ckin gida tana fadn ni banason sharri wlh , anty tace momy kenan ta dai tana son yarinyar nan , yace kin sani ne anty? can fa na ganta guraran badarawa tana tafe tana hada hanya kamar me maye, to karewa nine na buge ta kuma bany zaton taji wani ciwon kirki ba, anty tace kai haba? yace Allah kuwa shgarta ma in kin gani rin ta manyn karuwai, Allah dai ya shirya anty tace Amin, yaushe kazo? yace tun shekaran jiya ina nan kd . bani n.d.a bani jaji kin san mun kusan gama course dinnan kuma muna sa ran karin girma ne ,tace Allah yasa yace amin suka shiga ciki WACECE FARIDA JUMARE? Farida jumare 'yar asalin jihar yola ce kyakkyawa tamkar balarabiya , mahaifin ta malam jumare mutum ne shi mai tsananin son abin duniya , haka matarshi maimuna.'ya'yansa sune jarinsa don baya yarda dan talaka ya auri 'yarsa. ya aurar da yara 3 kafin farida daya tana aure a abuja anty sa'adatu, any lami tana kano tana auran wani shaharren dan kasuwa ne, sai anty amina da take port harcout mijin ta sojan sama ne mai babban matsayi yanxun burin malam jumare yana kan farida wanda duk tafi suaran yaranshi kyau . wannan yasa ya dage kan tayi karatun zamani don yana da harn shugaban kasa ne, itama farida har tafi mahaifinta kudi , tun tana karamarta take sheka ma 'yan makarantar su karya akn cewa mahaifin ta minister ne, amma da aka gane sai wasu 'yan makarantar tasu suka sa mata farida 'yar minister. a. secondary kuwa ai sai ta soma bin samari don ta samukudin siyan kayan kece raini,irin na 'ya'yan masu dshi, duk kuwa rin kokarin d yyyinta suke yi na ganin sun fito da ita cikin tsara. ta lakanci maza yanda ba'a zato in taga dan iska ko ince mazinaci tasan shi, tun da in har ta gane yana da kudi sai ta san yanda zata hada hulda dshi manyan mutane take harka dasu tana jan kudi. malam jumare yasan komai amma baya magana tunda shima yana shakar kudi, sai yaga hakan ma ya fiye mishi da ace auran tayi kai har da nasani yayi na cewa suma saura da bai aurar dasu ba tunda wannan hanyar an fi samun kudi (Allah ya kyauta). domin kaf unguwar su babu wanda ya kaishi samun kudi babu mai jan rin motarshi duk lokacn da farida ta smi hutu takan tafi abuja ko port a wani zuwan da tayi ne ta fita farautar masu bayan tayi dan yawonta cikin motar anty amina sai ta zame wani super market ta shiga ta gama sayendn yan kayan bakinta tafito jingina tayi jikin motarta tana neman lambar wayarwata kawarta 'yaryola da tayiaure anan port. din kanta gama wata shegiyar jeep ta tsaya gabanta kadan kasancewr idonta yana sanye cikin glass ya bata damar tsurawaa motar ido batare da an gane ba,musmman ma da ya kasance tana mai cigaba da dan danna wayarta ba kyanmotar ko kuma bata taba ganin irin motar bane a'a son take tfa mi motar irin nasu ne? numfashin tane ya soya dauke dan tsabar faduwar da gabanta yayi ba wai don ganin mallakinmotar ya kasance soja ba a' ba kuma ganin matsayin shina sojan ne ya tsorata taba sai dangnin kyau dacikar zati tasha hulda da sojoji amma bata taba ganin sojan da kuma yayi mishi matukar kyau irin wannanba cike (not clear) miskilanci tafiya daga ganinshi tasan zaiyi girman kai , tke sonshi ya shige ta har ta motsa, sun shiga cikin super market (not clear) a motarta ta zauna tana tunanin yanda zata ba da kanta gareshi karo na farko da ta soma tunanin bada kanta ga namiji ba dankudi ba.layin rashi ta soma nema cikin sa'a ksance itama. barikin soja take,a rude tace ganinan ki min taimako,hoton yaumar na nan manne a rana harta isa gidan rashida taimakon waya, a daddafe suka gaisa ta soma fadin taimakon da zaki min rashida yanzu naga wani gaye shima soja ne kyakkyawa mai mukamn sojanta fari dogo yana da cikar haltta, dariya sosai rashida takeyi kafin tace yaya sunan shi? farida tacenan fa daya, yanzunnan fa na ganshi gskya ina sonshi, ba xan boyemiki ba rashida tace ina zuwa , hotunane na sojoji kusan hamsin amma bataga wanda take neman bahakanne yasa tayi mata alkawarin bincika mata. duk 'yan kwanakin farida babu kwancyar hankali kullum tana zarya gidan rashda ko an samu lbrn sojanta.yau kam cikn sa'a tana sanye da doguwar riga baka dagyalentakyawunt nakara fitowa tamkar sun hada iri da larabawa , maza da yawasun so tayawa tun kanhanya taki sauraren su,burin ta taga sojanta , suna ckin hira da rashida a uwar dakinta wato bedroom , sunusi mjinta y shigo yana gayamata suna tare da abokin shi ne soja umar tasan shi sai dai shi ba'a wannn barikn yake ba tre suka fito tana cewa bari ta tafi amma me? tana fitowa sukayi ido hudu da sojanta cike da daga waya dauke kanshi , ta zaun tana gaishe su msawa daya sojan umar yayi bai kara magana ba, amma daya dan gota sai ya gane ta, duk da kallon tsoron da yayi mata ranar farko, kyawunta baya da saurin gogewa a idon mutum ya mata wani duba mai kama dana ranin wayo, kaman naso na gane ki ko? ta dube shi cikin nuna kamala da kunya irinta matan kwarai tace nikuwa? hakan ya birge shi yce gidan sojan sunusitadan dube shi sannan ta sunkuyar da kai, hakane. yanzun ma can zanje sai kuma mai mashine ya kawoni nan barkn yace ayya baki kulabane? tace eh ban lura ba da yake ma ba wai ina hawa mashn bane shiyasa duk na kasa skewa dadi ya kara kamashi dama shi bayason mace tana hawa mashin yace shigo inkai ki tace a'a ai nayi dare gida zan koma na jima ina yawo saeda baya ne na gane bama a barikin nake ba, yace to shigo nakai ki gidan tace ayi haka kai ma ai kana da wurin zuwa yayi murmushin da zuciyartaa kara tsinkewa da kara mustuwa cikin kogin sonshi yace ba komai cikin farinciki ta shiga. [1:34PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu1----7 Gidan anty amina suka je ya ce nanne gidanku? tace mishi nan gidan yayarta ne, ita yar yola ce yayi mata yan tambayoyi tasanar dashi duk game da krtn tane, tace yanzu tana universty,100 lvl tana karantar home economics, ya ce yayi kyau hakan domin ina da kishi da yawa ba xan bar mata ta tayi aiki ba. dadi ya kama ta kenan yana sonta, dan haka sai tace ai nima nafi san na xauna a gida dan na kula da mijina da tarbiyan yayana, yace ba xan bari sai wani lkc ba yaya sunan ki tace farida jumare,yace farida ina sanki domin na sami irin matar da na jima ina roqon Allah ,kanta a qasa wai ita tana jin kunya, wannan ce farkon fara soyyansu.ya umar yana tsananin san farida yaje yola har ba adadi, kuma yana kashe masu kudi duk da farida tana nuna badan kudin shi take son shiba. saidai wannan bai hana farida hulda da wasu maxan kamar yanda ta saba ba. cikin shekaru ciki ne ya umar yai ta samun matsayi daya bayan daya,har xuwa yanxu dayake saran xai samu muqamin captain. Zahiri farida tana son ya umar, saidai babanta ne bayaso tayi aure sbd kudin da uake narko mishi,amma shi ba dan wani krtn taba.farida ce kawai take ce masa haka.ni ko ayanxu nayi na daman irin shigar da nake yi da, saidai na bar shiri tun rani damin kaf unguwanmu har gidanmu bani da shaida,na daina saka duk wani wando inba na mkrnt ba,ina saka siket ne da xani tun faruwan wannan abin sai naji ina jin kunyan fita.satina daya ko waje ban leqa ba kullun ina kwance.ashe hankalin suraj ya tashi rashin haduwarmu gashi wayar daya bani tana cikin jakar nan,kuma kayan suna gidan su.gashi sanda muka rabu ina pushi sbd abin da yayimin.shi harga Allah ba nufinshi in mun aikata wannan xunubi ya barni ba. a ganinshi wannan baxai shafa auranmu ba.mu qoqarinmu muna koyi ne da nasara wannan shi xaisa mu kara kullewa. kullun sai yaxo layinmu can farkon layin ya tsaya da mota yana sauraran ta in da xan fito.yau ko dayaga an cika sati yar guntuwan wasiqa ya rbt tare da kayan daya saya min. Har da hotunan da muka yi a gun party da takarmi da jakar, nufinshi muci gaba da mu'amala ta waya, kotsam sai ya hango aisha yar autar mama,can tsallaken titi cikin wani shago,bread taje saya an xubo mata su cikin laida, taxo xata wuce ya tako da sauri ,aisha taja ta tsaya ta dube shi fuska babu walwala tace naam yace ina xaki ne? tace gida xanje, yace asmau tana nan? tace eh, yace taji sauqi ne? aisha cikin qosawa tace eh taji mana,yace gashi in baki saqo ki bata? tace to.mota yaje ya dauko wata laida ya bata sannan kice mata akwai saqo cikin jakar nan xan kirata, har ya tafi sai ya juya aisha, ta tsaya da sassarfa ya isa gunta kada ki bari kowa ya gani fa in tana cikin mutanene ki boye.tace to, bai san aisha da tsurku ba.kai tsaye dakin mama ta je, tace mama kinga wannan suraj dinko shi ne ya bani wannan wai in kaima asmau kar na bari kowa ya gani, mama ta ansa sannan tace aisha ta fita. kwarai hankaln mama ya tashi da taga abubuwan dake cikin ledar , irin kayan da ta gani tare da wayar, sai uwa. uba hotunan hawayen mama ya kwanceya soma zuba laillai Asma'u tayi nisa a haka Aina'u da fatima suka same ta sun dawo ne daga aken da tamusu, hankalin su yayi matukar tashi da ganin mma tana kuka domn bakon abu ne gare su, tsakiya suka sakata sunatambayar ta dalili sam basu lura da kayan ba ckn shasshekar kuka take fadin, nce Asma'u yawonta taje kun musa min to gashi dama yarnyar nan so take taga bayana su kansu sun sha mamaki ganina kwance jikn suraj muna rawaa hotunan kala 6 ne duka muna manne da juna guntuwar wasikar da fatima ta karanta tana magana ne akan ban hakuri akan abin daya faru tsakaninmu. yace don Allah kada ya zama sanadyar karshen soyayyar mu, kuma yace ga wayan nan zamuci gaba dajin juna a waya mama tace shi kenan ta lalata rayuwarta ta kuma bada budurcinta don haka babu ni babu Asma'u ku kiramin su hajiya su zama shaida. Anty Aina'u tace a'a mama wannanda ki rufa mata asir ganin wannan abin zi kara zubar mata da mutunci anangda kila ya fita cikin layin nan duk da hadin kan da muke da shi bai dace ba. Fatima ma tace gaskiya ne mama adai kirata aci ubanta amma kayan konasuza'ayi. inakwance kan gado anty fatima ta shigo ke kizo inji mama daga ganin yadda tamin kiran gaba na ya fadi,nasan bana arziki bane kiran. na shiga kayan nasoma gani a zuciyata nace innalillahi wa inna ilaihir rajiun, na shiga na zauna mama tadubeni sai hawaye tsoro ya kamani mama tana kuka saboda ni? nan nima nasoma nawa kukan ina fadin na tuba mama na daina don Allah mama ki yafemin mama cikin rawar muryatace na yafe ma suraj ke tunda har kinsan kibi namiji ki tafi gurin party nace banjeba wani wawan mari anty aina tasakarmin sannan anty fatima ta watso min hotunan na zaro idanuna cikin tsananin fduwar gaba numfashina ya kusan daukewa shi kenan bakina ya mutu ina sauraron duk hukuncin daza a min dole na dauka anty aina tace fatma kwashe kayan za'a nuna ma alhaj dasu ya abubakar nasa ihu ina rokonsu , mama tace ai gara ki tona ma kanki asir kowa yaji kafin nayi shiru tuni yan gidan sun soma shigowa dakin Allah yasa anty fatima ta kwashe hotunan da kayan sai takalm da jakan da wayar, anty aina suka ce suraj ya aiko min dashi kenan har yanzun muna tare. a raina naji dadin yanda suka rufamin asiri, na yarda naka sai naka kuma hannunka baya rubewa ka yanke ka yar su hajiya da umma sun bada hakuri amma mama tace ita fa in nemi uwata furucin ya tayar min da da hankali tare da sakani nadama sai dai kash nayi nadamar a lokacin da bata da amfani tunda duk mutane basa min kallon kima da mutunci wani sabon tashin hankalin ma mama cema su fatima tayi su kaini asibiti a duba ni ko inada ciki haka ko washegari da sassafe sukayi asibiti dani, likita ya dubani ya kuma tabbatar da bani da komai ranar nayi kuka har na gaji nasan cewa Allah ne kadai shaidata kan cewa ban taba sanin 'da namiji ba. An nunawa alhji wayar da kuma jakar nan yayi Allah wadai da halina, tare da neman mahaifin suraj kan cewa dansu ya fito sun gaji da yaudarar daya kemin mahaifn suraj yace shi danshi bai isa aure ba don haka baza su mashi aure yanxun ba. alhaji yace amma ya isa yaudarar yaran mutane yana batawa, to suja mai kunne duk abin daya faru da 'yarsa shine . tuni na gane shi namiji komai yayi ado ne. suna na ya baci sai sa'a xan samu mijin aure, uwa uba gashi mama ko gaishe ta nayi bata amsawa su anty ana da fatima ko yaushe cikin tsangwama da zagina suke, na samu umma da hajya na rokesuakan subawamama hakuri amma abin ya faskara domin ce musu tayi babu yafiya tsakanin mu, hakan kara daga hankalina na soma tunanin inda zan samu mai taimakamn don ganin anba mama hakuri ina kwance don yanxu ko makaranta na daina zuwa, bana ma fita ko ina towa zan tunkara ince ya bani kudin mashine? bayan haka ina jinkunyar fita katsam saimomy ta fadomin a rai, dukcikin kawayen mama babu kamarmomy suna matukar jin shawarar juna anan take na mike akwatin kayana da jaka na soma nema zani da riga da zansa amma abin takaici duk kayana na duba ba bu zani sai kwaya daya nakai su an maida min siket. na dauka na saka sannan na soma saka shima banda na arziki dan garama na islamiyata shine ma yakai min guiwa nasa nafita ,duk na kade danko abincin kirki banaci ,gidansu momy na tsallaka na shiga nayi sallama gabana yafadi sakamakon ganin ya umar da anty amarya suna magana ta amsa min shi kam 'yar fara'an dana same shi yanayi sai ta dinke take yakoma tamkar bai taba dariya ba , dama gashi cikin kakin soja, don kunya take na tuno halin daya ganni kwanakin baya ji yayi tamkar in juya in koma amma sainayi ta mza nace anty ina kwan? tace lfy asma'u nace momy tana nan? anty tace tana ciki na shiga dakin momy tana zaune kan gado tana ninke kaya ,na zauna sannan na gaishe ta sannan na shiga kuka ina rattafo mata matsalata, tace nayi shiruzata shigo gdanda daddare, na tashi nacigaba danunke kayan tana ta min nasiha tare da jan hankalina, kan irnkayan da nake sawa , nace mata ai na daina yanzu ma inason anjima zan koma gida 5 ne in jamilaa ta dawo makaranta ta dan budemn kasancewar jamila tana dinki momy tace ki kawozan gaya mata inta dawo. kema da kin maida kai ai da uanzun kin iya tunda tare muka kaiku, nace ai nama kaina yaanzu ko ai nasan mama ba zata kuma asarar kudin ta ba. haka ko daa dare sai ga momy sun jima tare da mama sannan aka aiko shema'u ta kirani na shiga na zauna momy tace gaya mata laifuka na . hakika bankyauta ba nace na tuba na kuma daina , nayi alkawarin ba zan sake ba haka ne yasa momy ta saka baki mama tace bata da alkawari, sau nawa tana dainawa amma saboda rainin hankali ta koma, nace insha Allah na daina. Abba ya dubi anty amarya yace kinji na rantsemikibabu daga kafa kan baatu nan ba zan yarda ya kuma azumin nan babumata ba,ai shi mijin mace 4 ne in rabon shi ce ya aure ta gaba,na taba jinhaka? shi mahaifin yarinyar wace irin jaki ne? 'yarsa tasa mi miji yace karatu an yaardain anyi abin zata cigaba amma kace kai sai ta gama? dama aurennesa din nan ba wai sonshi ba ne tunda gashi muma muna da yaran a gda yazo ya aura. shiru anty tayi saboda ta ji abin daya fi karfinta tasan abba sarai dakafiya kan abin daya fada ssaidai yanxun bata san yanda zasuyi ba,ya soma neman layin umar, ringing na 3 ya dauka cikin girmamawa yace Abba ina kwana? ya amsa da fadin lfy lau zaka samu zuwa ne koko na fada maka ta waya? yace meya faru abba? abba yace zancan auran ka f? yace ayimin hakuri abba zuwa lokacin da suke s......ya katse shi da fadin yi min shiru ka kara da ita lokaci mai zuwa, ka turo dakomai na biki inma baza ka samu zuwa ba ya kashe wayarshi. ya umar ya tsorat da jin zancan Abba, yasan kuma yana nufin abin daya fada.ba zai iyaja da a bba ba don haka ya kira layin anty dan jin karin bayani shaida mishi tayi ya gagauta samun farida ko da aure ne mahaifin nata su yarda a daura in yaso ta tare daga baya,inko ba haka ba saidai ka dauki kaddara domin ga abb bbu fashin auran nan, zufa ta zubo mishi take hankalinshi ya tashi yace anty bari na kira fridan ina zuwa , ya kashe sannan ya soma kiran layin farida wayaar tana nesa da ita kuma cikin jaka , kai koda tana kusa ma zaiyi wuya taji domin bata cikin hankalinta, saboda haka har wayr ta yanke batta ma sani ba, ya kira [1:35PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu1----8 Abba ya dubi anty amarya yace kinji na rantsemikibabu daga kafa kan baatu nan ba zan yarda ya kuma azumin nan babumata ba,ai shi mijin mace 4 ne in rabon shi ce ya aure ta gaba,na taba jinhaka? shi mahaifin yarinyar wace irin jaki ne? 'yarsa tasa mi miji yace karatu an yaardain anyi abin zata cigaba amma kace kai sai ta gama? dama aurennesa din nan ba wai sonshi ba ne tunda gashi muma muna da yaran a gda yazo ya aura. shiru anty tayi saboda ta ji abin daya fi karfinta tasan abba sarai dakafiya kan abin daya fada ssaidai yanxun bata san yanda zasuyi ba,ya soma neman layin umar, ringing na 3 ya dauka cikin girmamawa yace Abba ina kwana? ya amsa da fadin lfy lau zaka samu zuwa ne koko na fada maka ta waya? yace meya faru abba? abba yace zancan auran ka f? yace ayimin hakuri abba zuwa lokacin da suke s......ya katse shi da fadin yi min shiru ka kara da ita lokaci mai zuwa, ka turo dakomai na biki inma baza ka samu zuwa ba ya kashe wayarshi. ya umar ya tsorat da jin zancan Abba, yasan kuma yana nufin abin daya fada.ba zai iyaja da a bba ba don haka ya kira layin anty dan jin karin bayani shaida mishi tayi ya gagauta samun farida ko da aure ne mahaifin nata su yarda a daura in yaso ta tare daga baya,inko ba haka ba saidai ka dauki kaddara domin ga abb bbu fashin auran nan, zufa ta zubo mishi take hankalinshi ya tashi yace anty bari na kira fridan ina zuwa , ya kashe sannan ya soma kiran layin farida wayaar tana nesa da ita kuma cikin jaka , kai koda tana kusa ma zaiyi wuya taji domin bata cikin hankalinta, saboda haka har wayr ta yanke batta ma sani ba, ya kira Yakira na biyu har zuwa na hudu bata daga ba, hankalinsi yaku ma tashi shiru yayi yana tunanin in shirinsu baiyiwu ba baisan irinmatar da abba xae aura mishiita ba, kila ma bata da tarbiyaa, ya tuno faridarshi abinsonshi kamilar mace,layinta yakaranema wannan lokacin sun gama masha'arsu kanta na dore bisa kirjin Alhaji sambo shahararren dan siyasa ne da kudi suka nem su mishi yawa,yanxun haka kujerar shigaban kasa yake, sai ko taji ringing din wayarta,kuma ringing namusamman da ta saka domin sojanta. da gudu ta hantsola duk dababu kaya jiknta ta ciro wayar ta daidai sanda take gabda tsinkewa tace slamu alaikum yyi aajiyar zuciya sannan yace kina ina nehaka baki dagawayata ba? tace sorry soja ina sallah ne yace ai da sauranlokaci gabanta ya fadi yanzu ko sha biyu batayiba tace walha nayi ina lazimi ne kuma wyar bata gurina, tana dakn na ne ni kuma ina dakin maman mu ne, dadi ya rufeshi yace kina ska mu cikin ddu'arki kuwa? tace Allah soja daan kai nakeyin wsu sallolin ina gayama Allah , domin banason in rasa ka, yace to yanxun ina mafita ? abba yasa min rana nan da sati 3 kafin azumi in gidan ku sunki yarda to shi zai aura min wata, sanin kanki ne ba zaniya ja da abbana ba, shwarar dana yanke itace ki amince sannan ki samu babanku ya yarda a daura mana aure, in yso in kin gama karatun sai ki tare (tashin hankali) domin yanda take son umar bata jin zata so kishiya don haka sai t yanke shwarwar tada ma mahifintabali ya amince koh auran a daura, don haka sai tace mishi zan kira ka duk yanda muka yi zakaji . sun kwashi sati suna rigima da babanta inda ya dage ba yanxu ba, kuma baiga kudin da sojan yake da shi da xai daura mata aure da shi? yace mata tasan nawa ya kashe kafim ya samu alhj sambo ya nemeta? shine sun same shi ko kudin da ya kashe ba a maida ba xata ce xatayi aure? to ai in dole ne auran saidai ta auri alhj sambo,domin suna saka ran shine xai xama shugaban qasa.waya tama sojanta ta sanar da shi baba ya ki yarda dan haka hankalinshi ya qara tashi musamman daya kasance farida tana ta mashi kuka, tace ko dai ta gudo ne gun shi in yaso sai ya samu wani malami ya daura musu aure? yace abbanshi baxai yarda ba,su dai cigaba da addu'a. sati daya har xuwa kwana goma ya umar bai ce ma abba komai ba,dan haka abba ya yanke shawaran samu amininshi alhjnmu domin yin shawara.ni ko tsautsayin xan kuma fadawa wani hali yasa nayi canjin jaka da samira sani yar islamiyarmu ce ta aje min jakaita kusa da tawa iri daya ne muna tashi sai na suri tata cikin rashin sani bayan an idar da sallar magariba. naje kicin gun da anty fatima take kwashe tuwo nida shemau muna kaima kowane dakin nasu kasancewar duk girkin gidan ko girkin wanene su anty fatima da anty aina ne suke yinshi,ka sancewar basa xuwa islamiya nakai na dakin hajiya ina dawowa anty aina'u ta qwalamin kira tarf da tambayata ina Alkur'anina? nace yana cikin jakata.na shiga dakinmu in aje tuwansu anty fatima sai na samu anty aina'u da wani littafi a hannunta tana jujjuya shi cikin mamaki, har xan fita tace ke xo nan,na isa cikin faduwan gaba matsananciya. tamiqo min littafin nan kuma kika koma? da sauri na ansa na duba bangon sai naga an rbt ILIMIN JIMA'I. gabana ya fadi nace ba nawa bane, ta daukeni da mari har sai da fitsari yaso ya kwace min dan xafi,ta miqe keda mama da kuma alhj,na kamota dan allah anty aina ki mini rai wlh ba nawa bane, takuma makamin duka tace yar rainin hankali kin saba yin abu kice bake ba ceko?na tafi lamo na kwanta ina tunanin babu mai yarda cewa ba nawa bane tun da na riga na fata sunana tun farko. Tun kafin a kirani na tafi dakin mama,na samu ta rabsa tagumi tana kallon littafin na ce wlh mama ba nawa ba ne,Allah kuwa......ta daga min hannu alamar inyi shiru ni kam tuni hawaye ya soma ambaliya,tace in fitan mata a daki,na koma dakinmu na kasa cin tuwan dama nida shema'u da aisha da hadiza muke ci,anty ana'u da anty fatima suke ci yau harda anty salima ta shigo.da alhj ya dawo mama ta same shi tace abubuwana sun isheta baxa ta iya ba,yanxu na koma neman sanin ilimin jima'i gara a min aure ta huta,kada in sa jininta ya hau,ta bashi littafin ya duba ya gani yasha mamaki sannan yace yasan abin yi.washe gari da safe bayan alhj ya karya didan abba ya shiga domin ya nemi shawararshi game da wanda xai bani a cikin abokansu, falonshi suka shiga suka gaisa.abba ya ce ina shirin shigowa sai gaka? alhj yace ai mi nan daka gani matsalace dani,abba yace nima haka,amma tunda ka rigani shugowa fara sanar dani taka.alhj yace wai cikin abokaou wanene mai mace daya?abba yayh dry yace meyasa kk tammaya? Alhj yace qara masa xanyi da yarinyan nan asma'u,gara in mata aure,tunda dan iskan yaron nan ya hure mata kunne,ta daina ganin kowa da gashi ni bama wannan ba,dubi irin littafin da take krnt wa,aiko kasan taso aure, abba ya duba yayi salati ya sallame yace duk nawa asma'un take data xama haka?xan ce tsarar jamila ce? alhj yace qwarai shekarunsu na sha biyar kenan.abba ya cf ta isa aure amma ga shawara,dama nima xancan da xanje maka dashi kenan ,yaran nan umar dubi har aliyu ya sanar dani yana san hadixan gidanka,salima sun sasanta da abubakar ga aina'u da fatima duk an gama magana amma yayansu kwata kwata sai shiririta, alhj yace yaya xance yarinyar da yakd nema? abb yace rabu da wadannan mutanan ba dattawa bane tunda ga matsala kawai mu hada su da asma'u su je can su qarata.alhj yace xai so asma'u kuwa? abba yace ya sota wata rana.alhj yace shi kenan sai a hada dana su aina'un ko? abba ya ce a'a kasan sati biyu na bashi to sati biyun xamu sa kafin axumin bana san xaman shi haka ba mata. kaga gara da da yanxu tunda ya samu qarin girman nan sai suka maida shi onasha can cikin arnan ma, alhj yace ai ya gayamin saidai ya ce course ne nan ma ba xai dade ba xai koma abuja,abba yace haka ne amma ai gara da yar uwarshi kusa.bani da lbrn halin da ake ciki sai dai najh ance momy tana kirana, naje gidan na same ta tana aiki su anty salima da jamila sunma duk suna aiki na rusuna na gaida momy sannan anty salima, jamila tace asma'u nace na'am,jamila xan xo kawo gyra.jamila tayi dry tace da an ganki anga gyaran kaya kamar da wani yace kiyi su sumiki kadan,nace babu dai komai ai na kusan gyara su duka bana san kawo miki duka ne.momy taxo ta jani xuwa dakinta tace min na xauna, na samu gu na xauna tace takalmina nanba nawa nake sawa? nace 38 ba tare da wani tunani ba tace wane kaloli nafi so? nace xaki saimin ne momy,tace eh,nace ko wannene inaso,tace shi kenan tashi kije gida,na fito dama tana tsame doyane xata daka saina sa hannu na s6a daka, tafito ta amshe ni tace naje gida. [1:38PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu1----9 Yara yaran gidanmu duk basu san me ke faruwa ba sai manya. mama ce ta qeqasa qasa tace yaran kirki ba xa'a bashi lalatacciya ba irina, ta kira momy tana ce mata su hada kai suce a'a, su bani wani can,momy tace sbd me? mama tace sbd asma'u dai kowa yasan ba yarinyar kirki bace. shiko umar duk layin nan shi masa albarka ake, ita fa? sai tsinuwa,dan haka in an hada an cuce shi,moy tace shi xakiyi shaidar shi? waliyi ne shi? dan haka ki barma wannan xancan,itama anty amarya tace gaskiya an qari dan gidata.gashi dama ba shiri suke yi da umar din ba, momy tace yanxu sa shirya in anyi auran, tace momy dama ke dai kina san asma'un nan, tace eh ina santa. abba ne yayi ma ya umar waya yace lalle ya bar komai yaxo, washe gari sai gashi. abba ya ce xancan auranka ne, kuma yaxo a qurarran lkc sai kaxo a san shirin da xa'ayi xufa ce ta keto ma ya umar, wanka yayi ta maxa yace ta abba ai da dan wannan ne dama anmin waya kawai saina turo ma anti kudi ta sai duk abin da ya dace, cikin farin ciki abba ya samai albarka. Abba yace dama nasan baxaka watsamin qasa a ido ba, yarinyar ma ta gida ce, asma'u ce yar gidan babanka alhj ahmad, gabanshi ya fadi da sauri ya dubi abba, abba ya ce yaya? ya umar yace a'a ina mamakin ta isa aure ne? abba yace qwararai shekara sha biyar ina laifi? takaici ya cika ya umar amma babu dama ya nuna, yace a'a babu laifi amma inaga gobe xan koma sad muna da training jibi. abba yace to kaje ku gana da matarka sannan abokanka su xama wakilanka anandin, yace shi kenan abba xan yi duka, daga nan dakin momy ya wuce ya sa mata rigima shifa baya san wannan yarinyar yar iska ce, momy tace kai na gari ne? yace Allah ya sani ni momy ina qoqarin kiyaye dokokin ubangijina, momy tace to kasa ma ranka ka auri mata ta qwarai, shiru yayi yana mamakin yanda su momy da abba basa kishin dansu. sunfa san halin yarinyar nan,amma sun nace,itama cewa tayi yaje ya gana dani sannan tace yasa abokanshi cikh kan ya tafi. ba ya iya ja da iyayanshi dan haka yace to momy, amma Allah yarinyar nan batada kunya. Ya umar yace kinsan fa ta taba watsamin ruwan datti? momy tace ai yarinya ce quruciya ke damunta, yace haka xanje ina fama da ita? tace ai xata daina ba xama tayi ba tunda taga daga kai sai ita, ya fita ranshi bace,kofar gida ya tsaya ya kira aminu, amininshi ne yace aminu ina jiranka nan kofan gidanmu, aminu yace captain umar kana kd kenan? yace eh dan allah kaxo ina cikin damuwa. kafin xuwan aminu sai ga ya aliyu yayi mamakin ganin ya umar dan ya kan kira shi ya sanar da shi xuwanshi, yace yaya yanxun kaxo? ya umar yace bari kaidai aliyu sai addu'a ba dadi ya kawo niba, amma shiga gun anty ka ce ta rbt abubuwan da ake so game da lefe da sauran abubuwa sai kaje ka cire kudi kuje kasuwa da anty, yace auran wa xa ayi? yace shiga kaji gun anty ko momy? aisha ta sameshi tsaye ta rusuna ta gaidashi sannan tace mama tace kaxo,yace to kice gani nan xuwa, tun dama shi dan dakin mama ne girma ne da kuma yawon aiki ya sa ya rage shiga gunta.ya shiga gefen mama ya nufa ya same ta xaune duk bata cikin walwala. Yayi sallama tace shigo faruk, ya umar ya shiga tare da fadin mama kina ciki? tace uhum ina ciki faruk, dama ina tunanin yanda zan ganka sai aina'u tace minute gka. waje shine nace Aisha ta kiramin kai, yace jiya nazo abba ne ya kira ni kan zancen aure, tace nima neman da nake ma kaa kenan , shawara zan baka kar ka amince da zancen auran nan, don yarinyar nan llaataccya ce, cikin mamaki ya dubi mama tace kana mamaki ne? nasan ba xan boye gaskiya ba in goyi bayan karya, ji nayi yana jin kunyar mama domin mace ce mai mutunci ba zai ya nuna bayason jininta a gabanta ba, domn ba zai manta lbrn da momy take bashiba takan ce haihuwrka kaawai nayi amma mama itace ta rene ka taci kashi da fitsarinka, lokacin bata haifi abubakar ba. haka sanda ta haifi abubakar din ma sai ta'aje shi ta dauke ka , shi kansa sanda ya taso yasan shi dan gidan mama ne sai shi ne ma yasa mata mama ya bita, tuna wannan da yayi shine yasa ya kara sadda kai kasa sannan yace mama ai yarinyar nan kanwata ce, kada ki damu mama tace kaima baza ka bani goyon baya ba? na sankaa faruk tund ka taso baka da mugun hali ita fa? ga rshin kunya a gunta kwani fatima tace min har ruwa ta watsa maka? yace ai wannan ya wuce mama kada ki damu, yanxu ina take dama dan ita nazo in hada ta da abokaina,ni muna da training jibi gobe znbi jirgin safe ne, Shiru mama tayi harga Allah bata so haka ba, don tasan ko itace ce abubakar zai auro mai irin halin asma'u baza ta yarda ba, kudi ya zube mata sannan ya fita, tace ai ni daka barsu faruk tunda momyn ka ta hana ka yarda da batuna, yana fita yaga aminu yazo sun gaisa sama sama sannan ya shiga rattafama aminu halin da yake ciki saidai bai sanar dashi yawon da asma'u keyiba, ya dai ce mishi bata da kunya, kuma yarinya ce karama. amma ko me kenan su hadu da dare. bayan sunyi sallama yace ta shiga gidan alhaji ta kiramai mara kunyar gidan yana fadin haka tasan asma'u ce, don haka saita wuce. a dakin hajiya a same ni muna kallon tashar MBC2 tace asma'u ya umar yana kira na dafa kirji [1:39PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Biyu1-----10 Nayi shiru hjiya tace naje bansan me kiran ke nufi ba, don haka yanda nake haka na fita hijabi kadai na saka sanda naje yana waya da faridanshi ne don naji yana cewakada ki damu farida ki sama ranki wannan auran dashi bababu duk daya ne zan kuma kira ki ya dan jima yana bata baki kafin daga baya sukayi sallama, ni dai ko a jikina tunda ban sn me ake ciki ba, yamin rin kallon dana tsana, tamkar yaga kashi, yace ke karama jeki canza kaya ba zaki shigar minute mota da datti ba, ban fahimce shi ba, don haka nace ni ban gane ba, yace ai ba zaki gane ba ya shiga gidansu nima na wuce gida, har naje daknmu na kwanta sai kuma nayi wani tunani kadanayi laifi ni 'yar sarkin laifi don haka sai naje na samu mama, nace ya umar yacena canja kaya na same shi, ni kuma ban gane nufin shi ba, harara ta sakar min sannan tace ai da wanda zakuje party ne baza ki zo ki gayanba,jin haka yasa na fita. shadda na saka riga da siket green , na saci hijabin hadiza na saka,saboda yafi nawatunda ni duk cikn hijabaina babu dogo. dga cikin zauran gidan mu ina kallonshi yana waya, a raina nace Allah mutumin nan mugu ne ,jibi yanda yake wani shan kamshi yana waya ma kenan shiyasa na tsane shina tsaya a kofar gidanmu ,yana gamawa ya dube ni cikin hada rai a raina nace donka ganni da kananan kaya ai ba wani ka gnni ba, na isa gurin yana kokarin bude mota ya shiga, sai ga abba ya fadada murmushi ganinmu tare yace sai ina haka umar? yace zan kaita ne abba ta gwada wasu takalma , abba yace to Allah ya shi muku albarka , gabana ya fadi na dai durkusa na gaida abba ya amsa sannan ya isa gurin motarshi ni kam kaina ya daure da yawa, ya umar ya shiga motarshi nima na kama gaban xan shiga yace karki yarda ki shigo min nan ni sa'an ki ne shiga baya, na shiga na zauna, Allah ba don ina tunanin kada na koma gida inyi laifi ba, Allah bazan bishi ba, don dai ni a gidan mu bani da 'yanci yin abu komai kankartar sa, shi kenan nayi laifi, don kuturun wulakanci muna cikin tafiya sai cemin nayi maza in saukar mishi daga kan seat in tsugunna kada agan mu tare sunan shi ya baci, raina yayi mugun baci har kwalla suka soma zubomin haka na tsugunna gurin aje kafa. Bansan ina muke tafya ba saidai naji ya kira farida, suna hirar soyayya, a raina nace har na tausaya miki ko wacece wannan faridar baki san shi bane shiyas, aini dan auri y umar gara na mutu b mji, can naji ya kira doctor hassan yana fada mishi gashi nan zuwa koda mottar ta tsaya ina nn inda nake nafi minti 30 kafin naji an bude min kofar motr yace fto daa Allah I ni wannan sai na kaita wurin car wsh, ni dai na fito kafafuna duk sunyi tsaami yace wuce muje sai kace ya Allah tasha wani zunbulelen hijabi, fir'auna a zuci musa a baki, ban dai tanka ba yayi gaba na bishi a rana nace to wanene aka kwantar a nan asibitin,, dan naga an rubuta (dirman hospital). office din da muka zauna ba kowa, can lkitan ya shigo wani dan dogo fari, yace ku shigo? ya umar yace eh gatanan ya nuna ni ina zaune can gefe likitan ya dubeni ya jima yana kallona tamkar mai nazari, har dai na gaji na mishi kallo da yake nufn kallon fa? yako gane sai yace captain umar kanwar nan taka ta cika tsiwa, ya umar cikin daurewar fuska yacekayi abin da muka zo y , ai da'a tsiwa ta tsaya da sauk, na dubi ya umar abin shi ya soma isata, ya ballo min harara na sunkuyar da ka, in ya hade rannan tamkar zaki nake ganinshi. likita yace to ina zuwa nidai sauraron abin da za'ayi , fita likitan yayi bai dade ba ya dawo dauke da allura da sauran tarkace, ya tsaya kana kawo hannunki? ni uwar tsoron allura don da amin allura gara na mutu da ciwona, haka nakan fadi in bani da lfy, ance muje asibiti amma yau gashi dan kuturun wulakanci lfy ta lau an sako ni a mota gurn sa kafa za'a min allura, tsawa ya umar ya min ki ba da hannu akace, nace to ni me za'a min ? kai tsaye ya umar yace gwajin kanjamau, na mike tsye da sauri saboda sai naji kamar nima a nan za'a sa min ciwon. ya umar ya kuma daka min tsawa ina zaki? na soma kuma ni bani da koma ban karasa ba naji saukar mari, tuni na nutsu. likitan yace bi ta a sannu , ya kama hannuna yasa allura ya cako jinina, suka fa tare suka barni ina ta faman kuka, a raina nace kila ma sbd ya tsaneni ne shine zai kala min sharrin cuta,kusa awa daya ya umar ya fara shigowa yace in naji kin fada ma wani inda mukazo, Allah sai kin gane kuranki, ni dai ban tanka ba sanda likitan yazo ya umar yana waya, don haka ya shiga 'yan rubuce rubuce bayan ya gama lkitan yace captain munyi gwaje gwaje kamar yanda kace bamu samu cuta ko daya ba,wato captan yarinyar tana da lfy sosai, a wannan zamanin damuke ciki samun yarinya ko ince a dari da kyar a samu goma, don haka bata da kanjamau kuma bata da sauran kananan ciwuka. y umar ya harare ni, wuce ki zauna inda kika zauna dazun, Allah ya taimake ki ya jima sannan ya fito ina da gangan yayi ta wani shegen gudu sai bigewa nakeyi da kujeru, naji mun tsaya sannan fa ya leko yace in fitar masa daga mota, daknmu na shige na kwanta kan gado na darsawa a raina bani da babbanmakiyi nan duniya kamarya umar ina ruwanshi dani don bin diddigi zai kaini gwajin kanjamau? a fili nace Allah ya isa. sam koda wasa ban sani wai ana shirin aurena bane , har sauran kwana hudu amma duk 'yan gdanmu da yaran sun sani sai dai ance kar su gayamin, don kar mu gudu da suraj , basu san yau rabona da suraj din ba tun ranar partyn nan. yau dinnan rahma tazo muna hira ina bata lbrn musanyar jakar da mukay da samir ban gama bamukaji sallama, ni dama ina daga ciki gurin da muke sallah kan sallayan ma nake. rahma tana daga bakin kofa tana kallon waje sanaj tace ka! akwatunan wanene wannan? waye zaiy aure a gidanku? nace nan gidan kuwa? tace ga akwatuna gud 6 rabin dozin? na mike na leka na koma na zauna hadi da tabe baki nace oho ,kila nasu anty aina ne kinsan ni yanxun a gidan nan agola ma ya fini daraka, komai sai dai inga anayi bana sani.rahma tace ba haka bane Allah suna sonki, sunf son suga kin canza ne nnace ba wani so dai ai sha'ani tsan ce kawai tunda in dan kaya ne tun yaushe na daina sawa? amma ko da safen nan sai da ya usama ya rarrankwashe ni sai kace nayi mishi wni laif, wai fa don kawai munyi karo, tace ni kin tuna min sai ga ya usman a gidanmu jiya wai yazo mu gaisa ,ni sai naga tuntuni kamar zaice yana sona nace tab ai wlh ki ka yarda kika auri ya usman shi kenan ni da ke danba zanje gidanshi ba, tace kai don Allag sbd me? nace allai ashe sonshi kikeyi? tace bai dace ba? naja tsaki. canja min lbr ni yan gidannan saida na kalle su kawai. rahma tace har mamaki kike bani, yayama za'a ce 'yan gidanku sanan su tsane ki ko ka kuma suki ki? nace duk abin da akemin a gidan nan haka ke miki a gidanku? kafin ta bani amsa Aisha tayi sallama muka amsa , tace anty asma'u kije inji wani mutum. nace kn san shi? tace a'a nayi shiru can nace ba suraj bane? tace a'a nace jeki. ce wanene? jim kadan ta dawoyace sako zai baki na mike rahma zo muje tace sai kin dwo nace don Allah ke da zo muje ta mike muka fita. yana tsaye jikn gidanmu sanye da jeans da shirt ban gane shi ba amma saimuka karasa, muka gaishe shinace kine kake nema na? yace eh sai na ke gann kamar na sansh, yace kn sann? nay dan murmushi sannan nace eh to na dai ganinna taba ganinka yace ok to n abokin captan ne nace wanene kuma cptan yace umr,nay wani bala'in hada rai, yanzu na gane shi shine wanda na watsa ma ya umar ruwa suna tare,cikinmasifa nace to lfy malam? yace kwantar da hankalin ki , sunana Al-amin nazo ne nagana da kawayanki don musan shirunku da abubuwan da zakuy,naja tsakinace kayi kuskure don ban gane nufinka ba, zo muje rahma nayi gaba. yace da rahma, zo ke ,tace Asma'u zo kiji nayi tafiyata, yace ke kawarta ce? rahma taceeh yace maganan bikinta kinsan angon baya nan. shine nazo naji bukatunku, kan rahma ya daure tace auran asma'u dawa to? yace da ya umar baki sani ba? rahma tace itama banyi zaton ta sani ba, yace shi kenan yanxu kije ku rubuto abubuwan da kuke bukata, tace anyaba kuskure bane? malam ina ga ba asma'un gidan nan bace, yace zan dai dawo anjiman. ni kam ina shiga cikin gdan naci karo da su anty amaryar gidan su ya umar ita da wa'yansu mata sai naji tace yauwa gama amaryar nan, ta nuna ni na kalle su cikin rashn fahimta, su kam sai kallona suke suna fadin tubarakallah masha Allah, gata yarnyar 'yar karama zai more aure,na wuce ni fa abubuwan da suke faruwa 'yan kwanakinnan suna daure min kai. na shiga cikn dakin umma na jiyo hayaniyarsu ina isa naga duk daukacin 'yn gidanmu ne illa mama. kadai ce bata gurin. [1:41PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: uska Biyu1----11 Duk suna kallon kayan a akwatina shiga ina fadin kayan wanene? duk suka duben, umma tace kayan ki ne shigo ki gani. na dafa kirji naceni? tace kwarai. anty aina'u tace wasa ake dake da za'ayi miki karya? nace to wa zan aura? shema'u cikin doki tace kinji dadinki yaya umar fa soja kai dama nce? ya umar fa kika ce ? fatma tace ki godema Allah kike wani ya umar,nace na shiga 3 ni asma'u , na mutu. fatima tace shegiya a irin wannan halinnaki ma ya rufa miki asiri da gudu na nufi daknmama tanakrga kudi na shiga a firgice nace mama wa ni za'ama aure da da yaya umar? don Allah mama banason shi ki taimake ni, tsawa ta daka minute yi min shiru har kna wani baki son shi an gaya miki shima sonki yke? to bari kji rokonshi akayi ya aure ki dan ma kada kije kina daga mishi hanci ki dube shi da kyauba ajinki bane. mamkn mama ya cikani,nasha zata a zuciya nake magana ashe ba hka bane, nace anya mama ku ne ku ka haife ni? saukar mari naji tare da fadn , tsinto ki mukayi, da gudu na fita dama ni uwar kwakwazo gashi ta same ni gurin ido , ihu na saka ba kukan mar ba sai na kin auran nan yau kam na kara yarda ba'a kaunata,ba'a sona na shiga 3!! haka nake fada da gudu 'yan gidan suka fito daga falon umma, hajiya da umma suka kama ni. Rahma ce me tambayataa rude menene asma'u? asma'u meya faru? umma tace kinji halinki aike asma'u sai kwakwazon tsiya baza ki fadi magana ba, cikin kuka nace don Allah umma ku taimako banason ya umar mugu ne Allah gara k kashe ni da kanku, anty aina'u tace dubi yar iskar yarnyar nan zai rufa mikiasiri da wannan mugun halin naki ya aura amma har kike fadin baki son shi ban sanlokacin dana ke meyasa baki aura ba za'abani, don ba'a sona ....duka suka rufeni dashi ita daant aina'u da anti fatima , da kyar su hjy da umma suka kwace ni, sunamusu fadan meyasa zasu duke ni na kufce nayi waje da gudu zan fita mama tana cewa kada ki fita gidannan,kcibis mukayi da yaya usman,nabi ta gefenshi zan shara da gudu ya damko ni. gidan uban wa zakije haka sa kace mahaukaciya?nace da dai ku barni in tafi, ya wurgoni cikin gda, mama da kanta ta dauki ice ta shiga muka min . rahma ta rungume ni tana kuka, mama tace matsa ko kema inmaka miki, su hjy suka shiga ssai kuka nake . hjy tace kin ja ma kanki duka a banza, cikin kuka nace ba'a sona hjy wlh an tsane ni. hajya tace ba tsana bace ke ba abin alfahari bane a gurnki? nace haba hjy wane alfahari? dubi yanda aka bar su anti aina'u sukayi ta karatunsu, sai ni ce za'a ma aure kuma maimakon aban wani sai a ban ya umar , wlh nasan kashe ni zayayi. Hjy tace wanene mugun?Umar din?Ban bata amsa ba na ci gaba da kukana.Rahma ma kukan take tana bani hkr,kafin wani lkc zazza6i ya rufe ni fuskata ta kumbura.Rahma ta ce bari taje gida ta sanar ma Momynta,ni dai ina kudundune ban san ma lkc ya yi nisa ba,ashe hr dare yayi. Muryar Momyn gidn Abba na jiyo wato Maman su Ya Umar,ta shigo suna cin abnci a barandarta da su Umma,na ji tana cewa Hjy Saude dk naji abn d ku kai ma Asma'u dan cin zalin a bi yarinyar da lalama abu ya faskara,sai ku taru kuna shigarta sai ka ce jaka?Umma ta ce to ai a gaisa tukunna ko? Momy ta ce ba ita na zo ba, Mama ta ce kina take sani ne yarinyar nan Umar sa'anta ne? Ai shi aka cuta ga mugun hali yayi biyayya ya hkr shi ne ita da zai rufamawa asiri zata ban da she shi ana kallonta? Momy taja tsaki yanzun ina Asma'un take? Hjy ta ce tana can dakin a nan Momy ta same ni ina ta rawar sanyi ga fuska suntum. Da sauri ta fita ta samu Ya Ali ta ce ya dauko motar Abba muje asibiti bn san asibitin da muka je ba na dai ji ana gungura ni akan gado,allurar da bana so yau kam na sha ta,Likitan ya ce zamu kwana don dan karamin ruwa , sannan da safe in ga Likitan ido Momy ce Ta kwana a guna duk d Momy ta aiko masu Mama cewa anbani gado,sai Mama ta ce ai ta bani mana ba ta zo ba. Da safe Anti Amarya suka zo da Abba,ya yi fada kamar me? Su Umma d Hjy sun same shi yana fadan ya ce shi ne sai a samu yarinya ai mata irin wannan duka sai ka ce jaka? Ai zanga Alhj Ahmad din zuwa yamma Likitan ya Sallame mu muka nufo gida, tun a hanya na ce Ma Momy ni fa wlh ba zan koma gidanmu ba,ta ce ai nima ba zan kai ki gidan Abba muka wuce dakin Momy muka shiga na kwanta akan gadonta tasa Anti Salima ta dafa min wake da hanta na danci. Da dare ta kira Ya Umar a waya landline ta ce bn d lfy mun kwanta a asibiti, ya ce Allah ya sawwak'e yanzu ina ina ne? ta ce gani sai na amsa nasa a junne Momy ta fita tana Murmushi ina dauka ya ce ai ni sun min dai-dai,Sun ma miki kadan sai ma kin yarda kin shigo hannuna.. Tun jiya na samu lbrn lugudan da aka miki, ki shirya zaman uk'uba,ya kashe wayar,na koma na kwanta kuka na saka,san da Momy ta shigo ta same ni ina kukan ta zauna ta dago ni me ya faru ne? Gaya min me ya ce miki? Cikin kuka na ce Momy don Allah ki taimaka min a fasa Auran nan,Wlh Yaya Umar ba ya kaunata don Allah Momyna,rumgume ni tayi tana fadin "kwantar da hnklnki Asma'u in har naga abn ba mai yiwuwa ba ne ba zan bari ba, ke ko anyi naga da kwara zan san yanda zan yi a kai,na ce Momy Yaya Umar ba shiri muke yi ba,ta ce ki bar ni da shi bana son kina mgnr kada ki kara cewa komai ba na so kowa yana cewa ba ki da kunya.kiyi shiru duk abin d aka ce ki ce to kin ji?Na ce to.Tunda muka yi haka da Momy bn kuma mgn ba,sai kuka. Rayuea kenan,yau ni Asma'u ni ce zan auri Ya Umar mutumin da na tsana ya tsane ni,Rahma da wasu kawayena sune Momy ta sa su samu abokanshi lis din komai,ita ce in bar su ai raba mugu da makami ibada ne,sun shirya Sister day saiwalima don ni da don ta ne ni da sun bar shi. Ana gobe da daurin aure a kayi sister day din,kin yin wanka ma na yi sai da Momy ta sa baki ta ce in yi wankan tunda shi ba ya garin ma,,,, [1:42PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu1----12 Dakyar dai momy ta lallabani nayi wanka ba don raina ya so ba, na danyi kwalliya amma raina a dagule yake, haka dai ake abubwan amma ina cikin damuwa a wajen sister day gaba daya hankalina yayi gida kawai dan sarari nake nema na samu mai machine ya kaini gida, Rahma ce take ta lallaba ni akan nayi hakuri har a tashi, sai da aka kusa tashi sanna Al-Ameen yazo shida wasu abokansu, bayan mun gaisa Rahma ce ta ce Munyi fushi sai yanzun hr an gama suka ce haba dai ta ce Allah munan ni gida zamu je ya dube ni to Amaryammu ya gaji ya?Na sakar mishi harara ya dubi sauran abokan ya ce kunga amarya tayi fushi ko ya matso kusa dani ya ce kada ki damu ya kara yin kasa da Murya, don Allah ba don ni ba kada ki bari wadannan abokan namu su gane halin da ake ciki.sbd basu san me yake faruwa ba.Hakan yasa na da daure na ce ina yininku?Suka ce lfy Amarya yaya jiki? Na ce da sauki Al-Amin ya gabatr dani Abdulmalik,Hasim,Sani,Sale sai Muhammad, na ce sannuku suka ce yauwa.Al-Amin ya ce me yasa zaki hau mashin?Rahma ta ce kasan bata jin dadi shi ne take so taje ta kwanta. ya ce to shiga mota mu kai ku,na ce ku bar shi ai kuma naga kun cika motar,ya ce bari wasu su sauka haka dai dole muka shiga. Muna isa bn jira komai ba na shige gidan Abba, na bar su suna mgn d Rah,a.Momy tana ta kiciniyar shigar ma d baki wadanda suka iso yanzn nan da abinci sai ta ganni tayi turus yaya dai 'yar gidan Momy? Na ce kaina ne ke ciwo gajiri,ta ce tofa,ina zuwa ta shiga da abinci dakinta ta fito,ta kira Anti Amarya ta ce bani makullin dakin Soja (Haka take kiranshi) ta ce Momy me za ki yi a dakin?Momy ta ce kwanciya matarshi zata yi ni dakina cike ke ma haka,Kin san kuma ba hayaniya take so ba,Ni ina cn ban son ma kome akeyi ba sai dai naga Momy ta bude kofa ta ce zo ki shiga 'yar Momy,ni dai bn ma san dakinshi ba ne tunda ni dai wayona ban san shi ba,daga baya nake ganinshi gwanin Kamshi na leka bedroom din naga ashe hr d Kofa ina zaton kofar ita ce ta 6ulla waje kusa d ta Ya Aliyu,na kwanta kn duguwar kujera idanuna fes suka sauka kan hotonashi sanye cikin kaki,na tsura ma fuskarshi ido yanayin hoton ya burhe ni hannunshi yana gefen kanshi alamar sarawa,na sani Ya Umar yana da kyau sai dai bana son shine na rumste ido ina tunanin zamn doya da manja da zanyi. Na tuna jiya jin wasu kawayena suna min murna nayi dacen mijin nunawa sa'a,sai wata ta ce ai bana sonshi,nan suka cika da mmk. Samira ta ce ke ko me yasa ba ki san shi gashi mai kyau gashi Soja mai mukamn Captain Samun irin su locky ne ke da ba kya gurin in kin tanka to na tanka,ina jin Rahma Momy tana cewa ina nan dakin,muna nan kwance muna hira jife-jife hr magrib tayi munyi sallah hr da Isha'i ai bacci ma ya soma dauka na sai kawai naji ana fesa min nono (wato salalle)ya Allah bakin ciki kamar me? Na saki kuka Momy ce ta zo ta hana,ta ce su fitar mata a gida nan ta lallashe ni bata so in wannan kukan nawa samin jikina ya tashi,tana dakin naji Abba ya kira ta tana fitowa naji yana ce mata nayi waya da Umar dole yazo daurin auranshi gobe in ma zai zi ne ya koma shi ya sani amma lallai ina son ya zo cikin jin dadi Momy ta ce hakan yayi in baya yazo ya tafi da matarshi,kwana nayi babu bacci addu'ata daya ita ce Allah ya dauki raina kafin gari ya waye a daura min aure da ya Umar,da safe zazza6i na tashi nayi kuka na gaji.rayuwa kenan. Misalin goma naji ana ga Ya Umar tamkar in bar gidan haka naji nan akayi ta shigowa da abubuwan tsaraba,su katan katan na drinks tun daga kan ruwa C way,hr zuwa kalolin Juice hakan ya faranta ran Momy da Abba hr Momy take tambayarshi ya sanar a gurin aikin nashi? Ya ce wlh Al-Amin ne ya dinga tura ma abokan mu da message ta waya,wadanda yasan Number dinsu,ta ce ai Aminu yaron yana kokari ko nan yana ta hidima da ita da kawayenta.ya mike yana cewa Anti Fa? ta ce tana can tana fama da baki 'yan Bauchi d Gombe duk sun zo ya ce bari in rage zafin nan ya dan tsaya ganin dakinshi a bude kamar kar ya shiga sai dai ya auno kai. lkcn ina kwance,Rahma d Jamila kanwarshi suna kallo.Ya tsaya yana kallonmu,ya ce kai waya ce ku bude min daki hr d kunna min TV? Cikin in ina Jamila ta ce Momy ce ta ce mu zo nan ta kashe TV ta mike Rahma ma ta mike suka fita,ni kam jikina ba karfi amma duk da haka na yunkura zan tashi jiri ya kuma yardani,ya ce min ke wace irin macacciyar yarinya ce??? Ki bari a daura auran mana kafin kizo ki tare, na mike sbd nan take naji karfi, na dube shi kamar zanyu mgn,ya zabga min harara,na duka da kai na fita ya rakani da dogon tsaki,dakin Momy na shige ina kuka tayi-tayi in gaya mata dalili naki,duk da kuruciyata ina jin nauyin gaya mata abin da ke tsakaninmu da ya Umar yanda take dawainiya dani an daura aure misalin karfe 2 gidn su Momy tankam da mutane,ni ko na kule can uwar dakin Momy ta shigo ta zauna kasa dani tasa hannu a wuyana,zafi taji rau ta ce haba 'yar gidan Momy wane irin zazza6i kenan? Ta shi kiyi wanka mana?Na ce Momy bakin ce baki gayyaci kowa ba?ta ce ai bn san wanda ya gaya musu ba ne,na ce ni sanyi na ke ji ba zan iya tashi ba,Momy ta yi tayi naki tashi dole ta barni na sha magani na koma na kwanta. Can zufa ta rufe ni da kaina,na tashi nayi wanka a bayi Momy na cikin daki ta shigo ta same ni nayo wanka ta ce yauwa ga Soja nan ya ce kizo ga abokan su na gurin aiki da su Al-Amin suna jiranki,ta tsaya na saka wani lallausan leshi fari mai fulawa blue ta bani farin takalmi da gyale da jaka na ce bar jakanan Momy. Momy tasa min zinari kirar Dubai ta feshe ni da turaruka duk da kasancewar ban shafa komai ba sai hoda ina fitowa mutane suka soma fadin kai Amarya ta hadu fuskata murtuk babu fara'a na ce Momy ina suke? Ta ce dakin shi ne ko falon baki ne je ki duba su Rahma suka shigo ashe 'yan iskan hr anko suka yi,kallon banza nayi musu, Shema'u ta ce kinyi kyau Asama'u na ce lallai Rahma kema kin shiga layin makiya na ko? Ta ce dana yi me? Na ce ga shinan hr da yin anko ko? Ta ce ayya don Allah yi hkr nayi mama ta dinka min zuwana kenan ko wanka da na kinayi Mama ta matsa min Shema'u ta ce mune kenan Makiyanki? To kije gida ki gani cike da 'yan uwana ne sa dana kusa,wata motar ma yanzun ta iso batun anko da kike yi namu dabn na su Mama daban,dn haka sai ki san makiyan naki suna da yawa naja tsaki a raina na ce kwaji da shi Momy ta leko ta ce Asma'u ba ki je ba yana ta waya wai suna falon baki na tafi tare da Rahma a kofar falon naga Al-Amin ya ce yawwa 'yar Amaryarmu kin 6oye ki zoga bakinmu suna son ganinki na ce gsky ba zan zhiga ba ya gaya min mgn a gabn mutane Allah zan rama na gaji, Al-Amin ya ce a'a ya Mafita muka daine abokan shi ne na can gurin aikin su, Na ce to ni wai ina ruwa na da abokan gurin aikinsu? Amin ya ce dan Allah ki taimaka in mun gama bikin nan lfy an fita kunyar mutane a san yanda za'ayi na ce ni dai in zaka taimaka min ya sake ni to,Al-Amin ba tare da wani tunanin ba ya ce to naga sun kalli juna da Rahma sunyi Murmushi na ce menebe na dariya?Harsuna hada baki gurin fadin babu komai. [1:44PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu1----13 Suka shige gaba ina biye dasu muka shiga falon kato ne falon abba amma cike da mutane suna ta ciye-ciyen kaji da abinci ga kalolin juce naji kunya sosai da ganinsu kadan kadn ko ina a hankali al- amin ya ring zag ywa dni yana gabartarw muna gam gaisawa ban tsaya jin wani dogon turanc ba nayo waje ina jin sanda dayan da akace sunanshi suleman yace amarya sai kinzo zamu yi namu bikin a can ban dai tanka ba. rahma ma data rako. ni nan baya na barota . sanda na iso tsakar gidan nannaga momy suna tsaye da ya umar da wsu kannanta yana mata baynin shi zai tafi tare da abokin shi sbd akwai abubuwan da zasuyi kila karin girma ne.momy taace Allah ya taimaka kaga abbanku? yace yaana tare da mutane ne amma xan gnsh yanzun tace to amaryar fa? yace ai zamuyi sallama tana can gurin abokan nawa , momy tce gta can ta wuce ya faga sanda nazo na wuce su amma sai yace bai kula ba, ya dubeni har kun gaisa kaina na daga yace to shi kenan ni zan wuce a raina nace kafi ruwa tafiya ,momy tace amma dai ba sallamar kenan ba ko? kai da kace sai wani satin za'a kaita ai ka bar mata wani abun sannan ku dan zanta. yayi shiru canyaace ko ina cike yake,momy ta harare shi dakin ka babu kowa ai. Ya dube ni sai kije ina xuwa na tsaya momy tace jeki dakin nashi ki jira shi kinji yar momy? hawaaye na nazuba shar na tad, ina zaune kan kujera na bar hawayena su zuba son ransu tunda ni nama rasa me zanyi inji dadi kamar yaqi ya shigo dakin ya dube ni, har da sauri nace kije ganinan sbd son maza. Allah yay wadaran mace mar kamun kai mara aji, to bari ma in shaida miki bana ga kanki yana rawa ba, tsautsayi ne yasa kika aure ni gabana ya shiga faduwa, yaci gaba shawarar da zan baki itace kada ki soma gangancn yarda a kawo ki gidana,domin in har kika yarda kaddara ta sa kika zo yayi dan murmushin mugunta , sunanki sorry kada ki manta kn tab watsa min ruwan dai fasiqa ba, sallah 5 rana aikn hajj da ummura shida duk bana mance rokon mace ta gari nasan Allah ba zai barni ba, zai amsa minute na dube shi idona jajur nce ka sakeni nima ai naga ba sonka nakeyi ba da kace kar na yarda nazo inda kake mezai hana baza ka fadawa su momy da kanka ba? yayi murmushin mugunta , ni inaso na gama da mahaifana lfy ba zan basu kunya ba , kuma bazan ki jin maganar suba kuma abu na karshe da xan gaya miki shine,zan aiko da komai kuma xan tanadar miki masauki zan bada motocin da zasuzo daukan amarya amma duk dan na faranta ran iyaye na amma inkin yarda kn shiga motor nanhar kika kai kanki inda nake ? yaja wani tsaki tare da fadin hum-hum yayi wani guntun murmushi Ya saka hannu cikin aljihun wandonshi ya ciro rafar yan dari biyar ya jefe ni a fuska da ita yace ga sadaka bance kada kije yawo ba, amma ki sani zina da aure babban laifi ne koda yake ke laifin gaba kikaa saka shi ba baya ba, zuciya ta ta baci nima cikin dacin rai nace ni di ba mazinaciya ba ce sannan in har ka kawo mata zan shiga kuma zanso don Allah kayi tsirena ba laifin ka bane, iyaye na suka jamini na saki kuka mai karfi yace kada kisake ki tara min jama'a nan gurin domin in har momy da abba sukaji abin da yake faruwa har ransu ya baci to saina kiyafi nasu baci domin ni nasan zafin bacin ran mahaifa duk karancin shekaruna nasan , habaici yayimin kuma kafin nace komai har yayi waje don haushi, kifa kaina nayi akan kujera ina kuka, is yaje yace ma momy wai gani can ina kuka bai san dalili ba, kuma ya rarrashe ni nakiyin shiru. momy tazo tana lallashina wai inyi shiru yace ya lallashe ni nakiyn shiru, ko dai zn bishi n? nace a'a kaina na ne yake ciwo muka koma dakinta na sha magani na kwanta. haka biki ya tashi ana ta son barka, amma ban dani da ango, kullum zai yau waya gidan yace a bani in amsa sai ya dinga gayamin bakaken maganganu, niko inba'a gabanmomy bane sai na aje in a gabanta ne sai na daure in hakura, har kwana 8 dinnan kowa yasan na rame matuka, ya aiko da kudin jirgi na kusan mutum 3 banda nawa yace a ciki har antyshi a cikin masu zuwa kai ni ranar tfiya da safe nasha kuka, tun ran sstters day sai yau na fito waje gdan mu kuma tun randa momy ta kaini asibiti ban kuma shiga ba sai yau su anty ne suka kaini amin fada, duk sunmin nasiha su umma da hajiya mama kam cewa tayi in naga dama in zauna in naga dama kada in zauna ita dai ai ta gaya ma ya umr in namishi rawar kai ya min dukan mutuwa. Alhaji ya min fada da nasha, kuma yace umar da yake namiji yayi na*am da wannan auran dan Allah kada ni in basu kunya, inko har na zama sanadin mutuwar auranbai yafemin ba duniya da lahira sannan kada na doso garin kd da sunan aurena ya mutu ko kuma yaji kai ganin gida ma baya nemana sai nan da shekara, ina ta kuka ak sani motar har filin jirgi rahma ta rakani da kyar aka rabamu. mun rungume juna muna kuka har sanda muka isa garin kuka nake, motoci ne sukazo daukar mu gud 2 duk sojoji ne drivers din, dma 'yan rakiyar anty amarya ne sa hajiyar gidnmu, sai kanwar mama inna shatu. Katon gida ne mai dauke da manyan flat guda hudu ginin iri daya ne ya tsaru, na farkon shine na ya umar nan muka shiga ta qofar cikin daga nan sai ka isa qatan falo mai masifar tsari da kayan alatu, yana dauke da dakuna biyu dayan a kulle danyan a bude,muka shiga na budan gado ne mai kyau da sauran tarkacan shi sai toilet da wordrop muka xauna ina ta lura wani yaro ne kirista dan qabilan ibo ya shigo mana da abinci ya ce oga yace ku jira shi ya fita.sun ci sun sha suka yi dani inci abinci naqi dole suka barni, inna shatu tace in sun tafi na ci nan muka kwana,sai washe gari da safe ya dawo ina jinsu yana ce musu legos yaje kuma bai samu gama abin da ya kai shi ba sai dare, shine yayo sammako jirgin qarfe shida suna karyawa suka soma shiri, kuka nasa suna ta lallashina shi da kanshi ya kaisu filin jirgi. farida ta xubama wayarta dake kan teburin gacnta ido,ga wani dogm tagumi da tasha, duk wanda yasanta yana ganinta yasan yau sai a hankali ba harka. Tunaninta daya yanxu sojanta yana can tare da yar iskan yarinyan da tsinannun iyayanshi suka xaba mishi,tana tsoro duk da yace sam baya qaunan ko ganin yarinyan tasan mace fa mace ce duk muninta musamman da ta tuna cewa ya sanar da ita yarinya karuwa ce bin maxa take yi danhaka baya sonta, inko xasu xauna tare tayi imani har ga Allah sai yarinyar nan tayi yanda tayi ta shawo kanshi ya saurareta. halama tana bin malamai, wani dogo tsaki da taja shi ya jawo hankalin alhj sambo dake ta amsa wayar shugaban masu kamfe dinshi yayi sallama da shi sannan ya dube ta yace na kula yau kina ciki damuwa farida,gaya min menene damuwar? kudine? ta ce a,a ta miqe tana cewa gida xan je yau ba xan dade a club dinnan ba. ya miqe shima xuciyarshi cike da yaudara idanunsa suna mata kallan sha'awa ya kama hannuwanta ya maida ta xauna, shin kin taba shan maganin damuwa? bai jira amsar ta ba ya balle hancin kwalbar giyar dake gabansa ya cika wani kofin glass ya miqa mata,amshi faridata duk wata damuwa ta duniya kinga maganita Cikhn xafin nama ta amsa ba tare da wani tunani ba, ta daga kofin sai data gama sannan ta aje ido ta tsura mishi tana ganinshi ya koma mata sojanta.murmushi ya ke mata irin wanda yake qayata sojan ya miqe ya kamata sannan ya dauki jakanta da kuma wayarta sai mota, tana ta mishi sambatu har suka isa gidan shaqatawarsa suka ci gaba da masha'ansu yanda suka saba,wal iyaxubillah.da safe ko sai gurin tara ta farka,jinta tayi wasai sai yar damuwar dan kadan, tayo wanka ba batun sallah ta sami alhj sambo yana karyawa dama shi mutun ne wanda ya ba ciki gsky da amana dan haka ga lodin abinici nan kala kala yaci wannan yaci wancan ya dube ta yar kyakkyawa ta kin farka? ta xauna da dan murmushi na tasg ya kk? yace lfy ba lau ba,da me ya faru kace ba lau ba? yace da farko wanene sojanki? kuma wanenf umar? ta mishi wani duba sannan tace menene? yace jiya na shiga gurare da yawa wanda ada baki bani damar shiga sosai ba,saida giya ta gaya miki qarya cewa ni sojanki ne tayi tsaki malam banasam binkice. Tunda dai ni ba matarka bace, kuma umar inka damu kasan shi to,ina mai farin cikin shaida maka shine xan aura. alhj sambo ya tsura mata ido.a ranshi yana raya aiko Allah bai qaddaro aure tsakaninsu ba, ta auri wani, baxai so su rabu ba, allah ya kaimu tace amin cikin isa.kuma daidai lkcn wayarta ta soma tsuwa alamar saqon waya ne ya shigo, ta ciro sai taga kiqan sojanta har guda ashirin da takwas tun jiya xuwa yau, koda ta duba sakon sai taga ban hakuri yake tare da lallashi yasan fushi ne ya hanata daga wayar amma ta saurari isowarshi yola nan da qarfe daya. ta dubi lkc qarfe goma ta soma tattara yanata yanata ya dube ta menene? tace babu komai gida xanje, yace bari inyi waya akaiki dan bai dace a matsayina na dan takara a ganni da mace ba, xai iya kawo min matsala ta gefen abokan gaba, tace bama sai ka kira kowa ba bari in tafi,ta gama shirya komai sannan taxo gabanshi yasan nufhnta dan haka ya soma neman inda ya ajiye check dinshi ya miqa mata, farida na yaba jiyan. [1:46PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu1----14 Dan haka gashi rbt duk yanda yayi miki ta tsugunna ta rbt dubu dari biyar yace sun isa, tace i, yace to nidai bana san abin da xai sa mu rabune, ko kinyi aure, tace dan wannan ai babu ji.Ina daki sanda ya umar ya dawo daga kai su anty amarya. nasan hakan ne ta hanyar jin danayo yana cewa yaran mai suna emeka yaje but din motarshi ya kwaso plantain, sannan yana son ganin shi tare da duk masu mishi aiki ma'ana sauran yan aikin su biyu,mai ba fulawa ruwa da kuma mai wankin motoci da shara ban da sojojin masu gadin shi.ban kuma jin duriyarsa ba har nayi sallar isha na kulle qofata na kwanta. sai fa da safe nayo wanka na gama shafa mai raina a cushe ga wata shegiyar yunwa da nakeji ta tun jiya raina bai gama baci ba, sai da na bude kayan sawana kaf babu nawa na gida, duka na lefe ne na dai dauki wani material mai taushi fari mai bulun fulawa na saka ina daura dan kwali naji wata irin dukan qofa tamkar xa'a karyata,tsoro ne ya kama ni na soma tunanin ko wani ne ya shigo ya umar baya nan? Amma sai naji muryanshi ce take fadin ke! ke! malama xo nan ki bude ma mutane qofa, kamar dakinta,da sauri naje na bude qofar yana tsaye da wando 3kwata,na kakin soja sai singilet itama ta kakin ce saidai mai santsi ce, fuskarshi murtuk tamkar hadarin magariba, ya daka min tsawa kallan me kike min? nayi maxa na kauda kaina.yace ta mara kunya yau Allah ya shigo da ke hannuna, xaki gane kuskuran da nace kada kiyi, gashi kin qiji kinbi san xuciyarki ta xaki sha wahala.duk masu aikin nan xan sallame su sbd abu 2,na farko kema ai yar aikince, sannan inma na barsu tunda kin riga kinsan dadin maxa to xaki kafa min xina a gida, dan haka na sallame su sai ki fito in nuna miki aikin ki,in kinyi kuskure daya ki sha duka. haka xaki yi ta bauta har my farida taxo kin dinga mata aiki, oya see your eyes lk a mujiya kina kallona a gurin,qaryan masifa kikeyi, na fito yayi gaba na bishi daga kitchen ya fara, gashi nan xaki dunga maku abinci keda masu gadi kada kisa dani dan baxan ci jagwalgwalonki ba. Sannan bana san qaxanta kada a barmin kitchen da datti falo a share agoge komai wanke toilet da gyara duk dakunan gidannan.sharangefanmu xuwa mota,sannan kakina dakika jiqa duk dadai basu bane yanxu suna cikin aikinki kina jina ko? hawaye yana xubo min nace to,yace in kin yarda na kamaki da wani kuskure sunanki sorry, ya juya ya fita. a raina nace azzalumi ya xanyi dole inyi tunda iyayana sune suka bada ni dole na haqura. da abinci na fara duk da cewan ban soma sakar mana girki ba ina ganin yanda su anty aina suke yi, dan haka na dafa ruwan tea na soya uban dankali sbd nasaba ganin na gidanmu da yawa,da makunsan ance duk abin da iyaye suke yi ko kuma nace ya mace duk abinda ake yi agidansu krt ne itama shi xata yi a gidan auranta.na gama na soma da dakina sannan falo na shiga kitchen ina gogewa ya umar ya shigo fuska tamke yace ina abincin masu gadin? na bude kula shaqe da dankali da qwai ya xuba min ido cikhm takaici baki da hankali dama nakula da haka,wannan uban abincin fa? Na xuba mashi ido cikin tsoro yace bar kallona da idanun mujiyanki a gun, na sunkuyar da kai yace ke da wanene wannan dankalin? na ce ta to to ban san yawan masu gadin bane, yaja tsaki ba xan dauki almubaxxaranci ba, dan haka sai ku cinye rar dare ga gun da xaki danna nan xasu xo su amsa ya fita na bishi da kallo yau ne na soma ganin shi da shadda ba kaki ba yar garke ja sai maiqo takeyi. araina nace ga mutun har mutun amma a cikin xuciyarshi mugu ne a mugunta bashi da abokin tarayya. na ci gaba da aikina na gama na fita na share cikin gidan sannan na hau wankin motocin guda uku ne duk na wanke, ban taba wanke mota ba sai yau a gajiye na koma kitchen na danna gun daya nuna min, sannan na xuba musu cikin wata kular na xuba musu komai cikin jug wato tea dana hada, na basu kofuna ya leqo ta windo ya ce gud mrng madam, na danyi fara'a kadan na ce, mrng naci gaba da aikina ya miqo hannu na bashi ya tafi.na xauna falo na soma karyawa kenan, na dubi agogo sha biyu a raina nace lailai na sha aiki. A raina nace lalle na sha aiki inko haka xanyi kullun aiki ya same ni, ni asma'u, ina cin abincin nan ina hawayen tausayama kaina,ina gamawa naje na kwanta, wani wawan bacci ne yayi awon gaba dani sbd gajiya ban farka ba sai karfe 2 da rabi ina ganin lkc na duro daga gado na shige toilet wanka nayo tare da alwala na idar da sallah na saka doguwan bakar riga na daura dan kwalin ban ko shafa mai ba sbd bashida amfani in tsaya yin wata kwalliya. na danna kiran maigadi sai gashi da sauri ya ce wldn madam ban ma tanka shiba na miqa mishi dankalin cikin wata kular ya miqo kayan daxun nima na diba na bude fridge, ina neman ruwa, sai naga ashe frixer ne shaqe da kifi,nama, kaji dadai sauransu na komo falo, can soqon tsakanin kujera da kujera naga wani dan mitsilin abu kamar fridge naje amma na kasa budewa.ina xaton ya umar dan kanshi ya aje wannan fridge din tunda daga gefen kujeran xamanshi take, na gane kujeran xamansa ne ta hanyar ganin jaridu da sauran takacan shi a kanta. Hatta phone landline a gefen kujerar take na koma kitchen na taro a gun wanke wanke na dawo haka na yini iar dare muka cinye wannan dankalin da qwai gyatsar magwas ta dame ni shi dai bansan shigowar shi ba ban kuma damu da in saninba. suna tare da abar sonshi,wanda ta canxa shiga xuwa atamfa yar holan da qaton hijabi maimakon riga da wandon da ta fita dashi, yayi lallashi tare da qara nuna mata tsananin tsanar da yayi ma amaryan tashi tare da qara karanto mata mugayan halayan amaryan,sannan ya labarta mata irin matakin da yayi niyar dauka na axabtar da ita, har sai wuya tasa ta kama gabanta.farida taji dadin hakan amma bata nuna ba sbd iya bariki, sai tace kar dai a tsananta fa,yace ke dai ki ta mana addu'a baba ya sauko duk randa kika shigo gidan xata bari.farida ta ce iyayanku fa? yace ko ban sake ta ba sai dai ta koma gun su da xama kiyi qoqarin shawo mana kan baba mu samu ya yarda kafin na koma abuja dan Allah ya sani baxan koma abacha barrack da wannan yarinyan ba.ya je yanemi masauki.. Da safe ya zo sunyi sallama in da ya cika su da kudi ya tafi jirgi ya biyo zuwa gida. Tun tuni ya dawo amma bai shigo ba sai 5 ni ko a wannan lkcn na gano wani dan fili can baya gurin da yalwar iskar Ubangiji ba kamar sanyi falon nan ba abu kamar hauka, AC 2 ga fankoki hr 3 bayan ko wani dan couredor na gani kusa da dakina na bi sai naga kofa ina budewa sai naga fili hr da 'yan fulawowyi da kujeru 2 tun da na gama abnci rana dama jalof din taliya nayi,ina gama wanke-wanke na dau abncina na nufi can. A can na yi azahae haka La'asar na kwanta kan sallayar na saka filo sanda ya shigo ya bi ta garejin shi na aje Mota anab ranshi ya soma 6aci sdb yanda yaga motarshi duk jirwaye duka 3n ashe 6acin rai na gaba sai da ya bude motar yaga yanda na lafge motocin da ruwa takaici ya ishe shi ya shigo ta kitchen bai ganni ba ya nufi dakin,shi ne hr toilet bana nan,ya dinga fadin ke ina ki ka shiga ne? Ke sam ni ban ji ba,bam san duniyar da nake ba,ina ta shara baccina ya ce lallai kenan hr ta soma zuwa yawon gulma a mokata don yasan ba za a bar ni fita ba sai da izininshi wato masu gadi hr zai fita sai kuma ya tuna da baya nan take ya zagayo ya fito bayan. Saukar Marin da naji ita ce ta katse min mafarkina da nake yi wai gani ga Rahma a mkrnt muna ta lbr. Firgigit na tashi tare da rike kumatuna tsananin tsoro ne ya ratsani.... Na zaro ido jikana yana rawa ya ce uban wanene ya saka ki ki jika min mota? Cikin in-ina na ce na na na wanke ne,hk ake wankin mota a garinku? Fuu!ya fita sai ga shi ya dawi da belt ya zane ni ya hana ni kuka sannan ya ce in yi ta tsallan kwado,ya fita ya saka direba da maigadi suka kai motocin gurin wanki ni ko nasha kuka hr na gode Allah da na gaji na fadi a raina ina tuba uwar wuyar da na sha gurin wankin motocin ban ta6a wanke mota ba ban san yanda zanyi ba,shi yasa nayi ta maka ruwa ko ta ina ina sa6o omo,jiya ma haka nayi na zata gida ya kwana yaga sun yi ne shi yasa yau ma na sheka musu ruwa ashe bai ma dawo ba tunda sanda ya fita ban riga na wanke ba. Bai kuma biyowa ta kaina ba hr bayan magriba na rarrafo na shigo ruwan dumi nasa na gasa jikina sannan nayo alwala.A zaune nayi sallah sbd kafufuna sun gaji, nan na kwanta kan abn sallar ina kuka,ni dai ban zo duniya cikin sa'a ba,bn d Suraj da Momy Da Rahma bani da mai sona ina nan hr 8 tayi nayi Isha'i tunda daji ne cikin Inyamurai ban ta6a jin kiran Sallah ba sai dai ka aduba agogo. Asuba ma dan dai jiki ya sa ba da tashi duk gajiya asubahi tana yi zan farka,na idar na koma na kwanta can naji tsawa a kaina,na tashi shegiya ba ki ba masu gadi abincin dare ba? an gaya miki gidana ana yinwa ne ko rowa? See translation [1:52PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu1----15 Nan fa gabana ya fadi na tuna bamma yi girkin dare ba,da sauri na tashi da gani sai zani da hijabin sallah Makaroni na dora nan na zauna a cikin hr tayi na juywe musu na kira su suka dauka na koma daki sanda zan wuce yana zaune kan kujera da dama na zargi cewa tashi ce yana waya da Gimbiyar tashi suna Syy Na gane hakanne ta hanyar kiran sunanta da yayi ya ce Farida my sweet heart kada ki damu na ce ban ta6a ganinshi yana fara'a ba sai yau na wuce daki a raina ina fadin bakin mugu. ************* Haka rayuwata ta kasance cikin wahala da bauta tun ban iya wanke mota ba har na iya, don ya ce ni zan ci gaba da wanke mota in nayi kuskure insha wuya wankin kaki ma na kware hr Azumi yazo ina jin shi ranar wata Asabar da aje saran ganin watan na Ramadan ina goge -goge a falo shi kuma ya na zaune yana shan tea. Da kanshi ya dafa, wayarshi ta soma ringin ya dauka,naji ya ce Momy ina kwana? Na juyo da sauri tunda na zo nan gidan sai yau naji ya ambaci sunan wanda na sani.tun da ba zama yake ba kamar in amshe wayar in ce Momy ki zo ki cece ni don Allah amma babu hali naji ya ce tana lafiya. Ai tana bacci bata tashi ba na sanni aka tambaya ya 6ulla min harara na ci gaba da aikina hawaye ya ce duk san da za ki kira Momy bana gida yau kuma bacci take kada ki damu Momy ai zamu zo da sallah in na samu hali amma zaku ga aike na Azumi a raba ma makota naku da na gidan Baba Alhj,kudi zan turo Aliyu ya je ya cire sai a sai komai hr na hidimar Sallah ko? Haka Momy tayi ya nacin son Magana dani amma ya Umar ya ki. Ranar Mndy ko ba ya nan na dauki landline din falo zan kira amma abn haushi ban rike number momy ba, sai fa gidanmu su kam kiran me zan musu suna Murna sun rabu da kaya.Don haka tsabar mugunta ranar Azumin farko dore nayi don ya ki tashina da yake ban san anga wata ba sai da safe na jiyo yana jin Radio ana fada a labarai shine na kama baki duk da ban ci komai ba. Haka Azumin yayi ta tafiya ban san in da yake shan ruwa ba haka sahur. Masu gadi ne kullum sai na musu da rana da safe direba ne kadai ke Azumin shima bn san inda yake Sahur ba,ni dai dama sai dai in na tashi akan lkc in dan hada tea insha in ban tashi ba inyi dore,akwai ranar da har na hada tea saina dubu a gogi naga ashe shida ma tayi ban lura ba kai da Azumin nan nasha wahala mara misaltuwa. Duk na rame na lalace na fige sai ido a waje na bakin shi yana cewa kamar na mujiya haka hr sallah tazo shi kadai ya tafi kaduna kan ita zuba ido ya ce in shirya shiru sai ma gurin direba naji ya ce Madam Ke ba ki bi oga kaduna ba?Sallah a garin nan ba dadi duk Hausawa sun gudu garin su na ce eh sai ya dawo zan je kai ranar nayi kuka hr na gaji dan nasa rai. Kwananshi 2 ya dawo ina kwance ina jin shi ya turo kofata ya jeho wata leda baka mai dan girma ya juya, na tashi na dubu ledar kayan miyan ne irin kuka, Ku6ewa, da garin yaji da daddawa. Sai Kuma wata ledar mai dauke da wasu tarkace kamar magani sai wasu wasiku guda 2 daya daga momy daya daga Rahma, na rungume wasikun ina kuka na soma duba ta momy. 'Yata ina fatan kina lfy? Na yi kokarin jin Muryarki amma soja ya ki, Sai ina ganin kamar yana wahalar da ke ne kada ki damu ina nan zuwa cikin watannan zan sa Aliyu ya rako ni in ganki. YA JIKI? Ya ce Kinyi 6ari kwanaki Allah ya ba da mai amfani sannan ga dan tarkacen mata nan duk kisha da madara sai na zo. Momynki. Shiru nayi ina mmkin Ya Umar,wai nayi 6ari? Kai namiji sai a barshi na ji dadi in Momy tazo kafarta kafata, ba zan zauna ba. Bayan na krnt ta momy, na kuma warware ta kawata Rahma domin itama naga abn da ta kunsa. Sis.....Asma'u Nayi Yi kewarki da zaton ki, Musamman a mkrnt Malamai sun kewarki hr gobe na kan yi kuka idan na kalli gurin zamanki a cikin ajin Islamiya,sai dai na ka ji dan dadi in na tuna Ya Umar mutumin kirki ne rike ki amana. Munyi jarabawa yanzu muna SS1 kuma ni da Ya Usman mun shirya don hr iyaye sun shiga ciki.A kwai labari da yawa sai kin zo bikin su anty Aina'u sauran sati 4,nasan kin sani. Aminiyarki, Rahma. Haka wasikar ta zamar min tamkar Kur'ani, kullum sai na karanta ina kuka ina fadin nima ina kewarki Rahma, ina kewar mkrnt.Rayuwa ta haka ta ci gaba da tafiya hr ranar wata Jumma'a na zauna kenan a falo sai ga shi ya shigo tamkar an jeho shi na tashi da sauri zan gudu dan ya min gargadin kan zaman falo,wata rana ya same ni ina zaune ya min duka sannan ya ce duk randa ya same ni sai ya harbe ni tunda bai hada falonshi da sunana ba. Don haka yau ma na ruga daki ina kokarin rufo kofa sai gashi ya banko na tsaya jikna na 6ari shi kanshi yasan ina matukar tsoronshi sai dai ya ce haushen da nake bashi ko zai kashe ni ba zan ce yayi hkr ba sbd tsabar taurin kai,ya ce ke da karfi na dube shi ya ce bari kiji ina ma dai zuwa ya fita can sai gashi da wata 'yar bindiga nan na soma sakin fitsari sbd tsoro nasan zai iya harbina, ya saito ni sosai,sannan ya kauce ni ya harbi bango nan na dauke numfashi na na fadi tare da salati ga zatona ni ya bindage ashe bango ya harba suma nayi sai da ya debo ruwa ya zuba min na farka ya san na kara tsorata dashi ina da daga kwance ya ce tashi na tashi da sauri ya ce Momy zata zo gobe kinga bindigar nan?na kalleta ta cikin tsoro ya ce yanda kika ga na harbi wannan bangon ya huje haka zan huda cikinki in har kika yi kuskuran gaya mata halin da kike ciki. Hawaye na zuba na ce bazan gaya mata ba,ya ce ke ki ka sani dai ya fita kai Soja babu imani. Duk da haka nayi murna da zuwan Momy da wuri na gama aikina ya ce yau ban da wankin mota,nayi wanka nasa sabon kaya wani yalon leshi mara nauyi,dama tun da nazo kayana uku ne, daga jallabiya sai atamfa da wani matarial wannan yayi datti in sa wannan,to wace kwalliya zanyi tunda nazo ko bakin gate ban taka ba,ban na ta6a ganin kowa ba daga shi sai masu gadi suma in sun zo daukan abncu,inazaune a bakin gado ina tunanin yanda zanga Momy,oh Allah yau zan ga na gida. Kiran Ya Umar na ji "'Ke!" Na taso da sauri ya dube ni na dan lkc sannan ya ce to haka yayi saura ki je ki saka sarka da dankunne kiyi shafe-shafen ku na mata,bana son ki yarda Momy ta gano halin da muke ciki za ki koma kwana dakina hr ta tafi na dube shi da sauri ya ce kada ki zata ko na soma sonki ne ba zan ta6a sonki ba,ya ci gaba zan daure in ci jagwalgwalonki hr ta tafi sannan yanzun in kin gama ki zauna nan falo zanje na dauko su,zan kara tuna miki kada kiyi ka sadar sanar da Momy komai dan nasan kanki zata yi fushi dani kamar yanda kema zan ha da ki da naki iyayan duk da ke baki dama d fushin su ba,amma ki sani in ba kya gidana sai dai ki shiga dny ce war Mahaifinki,ko fa da ki ka yarda Momy tayi min Allah in ta tafi zaka gane kuskuren ki,ya tafi dauko su haka nayi jigum a gabn madubi ina kallo kaina ni Asma'u wannan shi ne a dake ka a hana ka kuka,lallai ban da ya ki ina ganin har da sharri ake koya ma Sojoji, Da na yi kwalliyar sai naga nayi kyau,na juya kwayar idunana da Ya Umar ke kiran su na Mujiya irin idanun nan ne da kwayar su ke da girma kuma sun fito na sha jin mutune na cewa suna son idanuna,haka Suraj na saka sarka da dan kunne na koma falo na zauna ko in ce nadofanu ina kallon tashar Aljazira ina zaton ahi ne yake kallo ya tashi ya tafi dauko su. Sallamar Momy da Aliyu da Ya Umar ce ta dawo dani daga kallon,da gudu na taso ina tsalle na rungume Momy,itama cikin farin ciki ta ce 'yata Asma'u oyoyo 'yata,sai kyma naga ta ciro ni daga jikinta ta tsaya tana dubana, ta kai hannu wuyana ta shafa ramin kirjina ta ce wannan kashin wuyan fa? Na dubi Ya Umar ya 6allo min harara nayi saurin fadin tun da tunda ya Umar ya amshe tunda tayi 6ari ne nima na kakaro 'yar fara'a na ce eh mana ba?tun lkcn ne kuma bani da lfy ne ai Momy ta dube shi sannan ta dube ni kin zubar da jini ne?Daga ganin jikin nan naki babu jini na ce eh na zubar na kama hannunta zo muje ki zauna,Momy na ce ya Aliyu sannu da hanya ya ce yauwa Asma'u Ya umar ya ja shi suka zauna Momy ma ta zauna naje da sauri na soma loda musu abnci da na sha kala-kala ga.farfesun kaji ga na kan rago ga farar taliya da miyan kwai ga jalof din shinkafa momy fadi take sannu 'yata da aiki duk namu ne? na zuba ma Ya Aliyu komai ga mamakina sai naji ya Umar yana cewa Madam sbd yau kinga su Momy watan kin manta da ni ko? Na yi dan yake na ce to me zan zubo maka? Ya ce sa min Farfesun kannan na zubo Mashi na koma kusa da Momy nima na saka cokali cikin nata.... Muna ci na kalli Ya Umar ya harare ni,Momy ni,Momy ta kalle shi sai abu yake kamar hararar wasa yake min yana yi yana murmushi,Momy ya ce me ki ka gani? Ta ce Harararta naga kana yi, ya ce ai ita ta sani Momy da da ni ta ke cin abncin yau gulma ta tashi wato ta gan ki,ai Momy za ta ta fine .Ni dai sai naji abn wani banbarakawai wai namiji da Suna Hajara. Yanda na lura ya ji dadin naman kannan sai da ya kara,kun san yin girki yau da gobe kan sa mutum hannunshi ya goge, don haka da ba ma yi a gida muna gani in su Anty Aina suna yi akan ce muje muna yi musu irin jajjage ko yankan albasa ko su Alayyaho,hakan yasa na riga lura tunda ina sha'awar girki shi ya sa yanzun ba ya ba ni wata wahala.Bayan mun gama na ja Momy dakin muna ta hira na tambaye ta Rahma ta ce ga ma sakonta nan na hotuna ta ce kema ki bata naki, da zumudi na amsa ina dubuwa ina fadin Allah Sarki Rahma ina naga hotunan da zan bata? Momy ta ce ba ku ta6a daukar hoto ba ne? nayi saurin tuna gargadin Ya Umar (Da har zan ce yaushe na samu 'yancin yin hoto)Amma sai na wayance na ce mu da ke cikin bariki anya ma muna da gurin hoto,ban dai sani ba. Momy ta tsuramin Ido ,Anya dai zamannan naku da soja Baya takuraki kuwa? Ni Naga lalacewar tayi yawa Ne Nace bakomai momy Ko mai yanamin daidai gwargwado, abincima sai yadda Naso zanci (A Raina Nace farin abinci bazan Kona namanshi ba; dakanshi yake duba store da firiza duk Wanda babu xai kawo haka drinks)tace shin kodai yana matsamiki ne? Nace a'a momy sai dai Ko Xaki rokarminshi yasani makaranta,Amma fa kadafa kice ninace fa Sabda namishi magana yace a'a yace to Xan mishi (a Raina Nace Allah dai kasa Yaya ya ambience). Munyi magariba da Isha'i tuwon semo na tuka mana da miyar kubewa busasshiya Ga man shanu dayazo dashi damuna cinema yake cewa momy baban farida nema yabashi sanda yaje yola.momy ta tabe baki haryanzu haryanzu kuna tare da farida? Yace to momy aydama ba matsalar tabace babantane kuma yasoma sakkowa, momy tace to kudai kuka sani nidai bazan yarda da batun wani Aure dai yanxuba, sai Naga kamun ludayin yata a gidan nan, ya cire hannu a cikin abinci Kamar ya'ya momy? Ta ce to ganin farko da zanyi Mata banga tasiriba,ta Kara baki ta rame sai idanu a warwaje .yace tonidai gatanan Ki tambayeta me nake Mata? Don ba a satina hudu da auranmu kikaxoba kafin tasamu cikin Nan Kinga Kyan datayi Ga kiba Kamar tafashe. Amma Tana samun cikin Kullum muna hanyar asibiti, kaina sunkuye anata keramin karya, momy tace kodai batacin abinci ne? Yace tanaci Badai Kamar daba momy tace itama haka tace Toh Allah ya kyauta sukace Ameen. A kitchen ya sameni Ina harhada wanke wanke yace ke dakina zakizo kuma karki soma zuwanmin da datti batare da yajira amsa taba ya fita. Bayadda zanyi haka nayyo wanka nashafa turare na dakko kayan Bacci nasaka dama bantaba saka rigar Bacci ba mai ya, na taje gashina danma Allah yasa gashina mai kyaune Amma da yadda ba kitso ba saloon din Nan ay da ya lalace na daure da ribbon na daura zani akan kayan nasaka hijjab na zauna kusa da momy tace tashi Kije gurin mijinki nima Bacci zanyi saida safe Haka naja Mata bargo nakara Ac najamata kofa daidai kofarshi Natasha duk tsoro ya cikani kilafa Yau nasha bakaken maganganu ,na tura kofar ahankali tamkar mai tura kwai na leka yace shigo mana cikin tsawa ya fada, nashiga na Maida kofar narufe natsaya Ina raba Ido Ina kallon shahararren dakin mai mutukar tsari komai nadakin sky blue ne, tundaga gadon har shinfidun xuwa kafet da labulaye zaune yake da Riga da wando na Bacci a gaban computer idanunshi sanye da glass, nazauna kasa gefen kofar Ina karema dakin kallo hoton wata kyakkyawa nagani Tana sanye da bakar jallabiya ta rufe kanta da gyalen, Nan kuwa na tsuramata Ido tamkar jinsin larabawa kusa da hotonta Shima nashine yayi kyau cikin kakin sojoji, bansan yaxo kusa daniba sai dai jinsanayi ya shakoni cikin hijab ya ruko wuyana yajani har gaban gadon, yasaka hannu ya ciro hoton wannan matar yace rike na rike da sauri yayi kasa da murya. Matata kenan farida, yaki ka ganta? Gaya min? Da sauri Nace Tana da kyau Nace shigarfa? ta menene? Nace ta mutunci, yace to mutuncin ya mace kenan shigar musulunci ba irinkiba ya Maida hoton ya dauki filo ya wurga min can sakon gadon da bango je can Ki kwanta Sbda gadona bana kazanta bane. Na kwanta da hijabina sbd sanyin AC na shi yayi yawa.Can cikin dare na farka sai na ganshi yana ta nafilfilu daga gurin da nake ya juyo min baya ne,na tsura mishi ido.Ya Umar yana da kyau ashe yana da Ibada sai dai mugunta,o Allah ban koma baccu ba har sanda naga ya gama ya kwanta,ya dauki waya ina jin shi ya lalubo abar son tashi hira suke ta masoya ina zaton ana nema take gaya mishi zata je fatakot dan yin shawara da Anty Amina game da batun Auran su,shima ya nuna jin dadin shi da yin haka sunyi sallama in da yake ce mata ta yu mafarki mai dadi yana kashe murya tare da kwantar da ita,hr mmkn shi na riga yi, bacci ya sace ni naji an shure ni na tashi firgigit! Tashi kiyi sallah har naje Masallaci na dawo kina nan kina aikin bacci,tun jiya ko juyi ba ki yi ba,kina ma sallar kuwa? na daga kai alamar Eh. Na tafi ina mmkin ashe akwai Masallac ni dai bn ta6a jin kiran sallah ba,naje zan shiga bayin shi ya ce wa?Maza na ki yanda cututtuka suka cika gari? Na ta fi na yi sallah sannan na gaida Momy na shiga kicin.Satin Momy daya suka soma shirin tafiya,kan su tafi sai da ta ce lallai ya Umar ya nemar min mkrnt ya ce zan shiga amma sau mun koma Abuja,sbd nan duk sai a hankalu,mkrntn haka su Momy suka tafi suka bar ni da kewarsu,na koma kamar da uban aiki ga masifa in nai kuskur naci duka da gwale-gwale cikin haka rannan ina fashin sallah na kira masu gadi ta hanyar dannan kararrauwar kar6ar abinci su,daya yazo na bashi naira 500 na ce ya siyo min always,kudin d Momy ta bani dubu biyu,ya dawo kenan sai ga Ya Umar ya tambaye shi menene? ya zo nema ya ce na aike shi ne ya amshi sakon ya shigo dashi ya duba yaga always,ya ce dama su kike aiki siyan wannan abn? Na ce na'am ya ce ina wasa dake ni,ina ina miki mgn kin ji sarai ki dinga wani na'am sai kin sani na ce au ba da shi nake amfani ba tsumma ne nake amfani,ya ce to yanzy ina kika samu kudi ko kin soma sata ne? Da sauri na ce a'a Momy ta ba ni ya ce to bani su na ciro na bashi ya wuce,haka na zauna gidan nan kullum addu'ata Allah ya kawo karshen zamana a gidannan. Ni ban sani ba ashe tun da Farida taje gurin Antynta Amina ta mata fa da ta ce ki zauna rayuwarki ta kare abn maza su in ba ki sani ba da kin tsufa shekarun ki sunja shi kenab sun gama yayinki gara ki je ki bude wuta ta ce to ya zanyi da shi na gaya mishi halin da kuke ciki zai goya miki baya to ko je gurin Baffan ruga wane ga baban nasu kuma ya bata dama ta turo mai sonta nata don haka ta kira Sojanta kuma ya amsa sun gana da Baffan kuma an ce tura manya yaje ya samu Abba,Abba ya ce ba ruwanshi da wannan mgn,sai ya nufi gurin Alhj, Alhj kam ya goyi baya shi nema ya shirya ya nufi yola inda aka yanke mishi sadaki dubu dari nai ga tsadar ta ba tunda ya san zauki Amarya dal a leda ana mishi tunanin an saka rana wata 4 a lissafe september kenan biki zai kama. Duk da gargadin da momy ta yi ma Ya Umar ya barni in zo bikin su Anty Aina sai ya ce mata to tana tafiya ya ce in dai ban yi kiba ba ba zan je ba.to ban ma san takamaiman lkcn bikin ba shi dai nasan yaje.A kwna a tashi gashi mun shiga October shekara daya da wata kenan da yin auranmu kuma lkcn ne ya Umar ya gama course din shi tun dare ya ce min na shirya kayana washe gari muka dauki hanyar Kaduna a mota.Direba ya jamu ya mu gun ja min kunne kan cewa kar na sake aji wata mgn a bakina,ni dau farin cikina zan je gida.. [1:53PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu1----16 Duk da ba sona iyayena suke yiba,hakan ba xai hanani shiga na gaishe su ba.mun cika mota da tsaraba sai gurin isha muka iso duk da shegen gudun da mukeyi tare da sammakon da muka yi amma sai da mukayi dare.wannan gari da shegen nisa da gudu na shiga gidan momy ta idar da sallah kenan na fada mata ina ta murna nayi sallolina kenan ina cin abinci yau dai jina nake tamkar na fito daga kurkuku.sai ga rahma ta muka rungume juna sai kuka, momy tayi tayi in shiga gidanmu naqi nace saina huta ai suma basu damu dani ba, da yanxu ko yara ne sun turo, in ina wannan maganan momy dry take min tace quruciya ce, haka sanda taje tana ji ina tambayar kowa ban tambayi yan gidanmu ba, tace baki tambayi su mama ba, nace bayan qilama basuce a gaishe ni ba? momy tayi dry tace sunce a gaida ke mana,dakin antx amarya na kwana ta ciromin sababin dunkuna wai inji ya umar kada nayi kada nayi amfani da kayana, na gane hikimarshi dan kada ace baya min dinki.washe gari na shiga gidanmu bayan na karya. Hawaye taf idona bansan ko kunan menene ba, haka suka xagaye ni suna min sannu dana shiga dakin mama ina ganin ta na saki kuka, ita dai kallona take nasan raman da bakin dana qara take kallo, yan gidanmu duk sunyi qorafi kan ramata, nidai bakina qanin qafata inji yan iya magana,ina can har dare na tashi na dawo.momy ke cemin ashe ya umar xai yi aure? duk da ba xaman dadi muke ba saida naji daban,nace ai banma sani ba, shine take ban rabarin sunqi yarda alhj ne mai shige mishi gaba nace Allah sanya alheri kada ki damu momy danni babu matsala,nidai ki mishi xancan krt na tunda ynxu abuja xamu koma ni konan kd ne ma ya barni.momy tace a'a babu batun kd yaxo dai ya min magana daya in baxai saki mkrt bane yamin bayani. ya umar ya sha fada gun momy na cewa bai gayan xancen auranshi ba, duk da yayi qaryar cewa baya ran raina ya baci ne,shi yasa yaqi gaya min haka nan tasa shi ya sai min waya mai kyau bansan yana qera gida a kd ba saida momy take cemin ai yanxu an yanke shawara inya gama gininshi na badarawa. In ya gama gininshi na badarawa nan xa'a min daki,nace au momy dama xa'a min daki? tace xa'a a miki man cae dinma ai shine yaqi,yace a bari sai kun dawo nan arewa naje gidansu anti aina da gidan salima da fatima. rahma ce ta rakani,randa xamu gaida momynta mun ba ta guri layinsu suraj ance tunda kika yi aure iyayanshi sun rasa gane kanshi, amma sun maida shi krt malesia, nace xaije ya qara lalacewa kenan, agaban suma ya bi mata bare wata qasa? tace lallai kam, nace ai ni inda ya suremin daya nuna yanasan jikina, kinsan fa nan duniya na tsani namijin da xai nuna yana san jikina. rahma tayi dry tace da kenan yanxu ai dole ki sakarma saja.na dubeta wane wai ya umar um ayi sha'ani dai kawai, tace da fatan ba gudun miji kike yi ba? nace rahma dama ina so mu kebe kiji damuwata,sbd anan duniya kece mutum daya dana ke fadama damuwata, kamar yanda kema nasan duk damuwarki, tace hakane, na kwashe komai tsakanina da ya umar na gaya mata sai da tayi kuka,dan tausaya min sannan tace cabdi yanxu tao ke a wace tuqa kike, Kada fa kije gashi yanxu shi da matar shine suyi ta cin xarafinki? nace ai ina ganin xan gaya ma abba ne qila ya kashe auran nan tunda sam baya qaunata, bakiga yanda na dawo bane? tace yanxun ma aikin danyi kyan gani,amma batun gaya ma abban shi ba ita bace mafita,sbda yana nuna yana kula da ke sannan yana nuna sanki gaban mutane, ta ki barshi shi da Allah ba azzalumin bane,akwai ranar qin dillanci yanxu dai ki sa krtn ki samu ko can abujan ne,in kin tafi ka kya gidan ma bare kiga haushi,in kin dawo kina daki,nace Allah na tuba rahma haushin me xanji naga nifa ba sanshi nake ba ina ruwana da matarshi? tace to sai abu nagaba.addu'o'ikin shagala da yin nafilfilu,nace acan ina san tashi amma ba xan iya ba naci aiki na gaji kamar jaka, tace yanxu sai ki tashi kiyi ta addu'a,Allah ya kawo miki sauki Nace hakanne magani na gode. tace,ai ni ma xan dinga taya ki addu'ar, Allah ya sani ina sanki da ya umar saidai kuma yanda Allah yayi ba makawa, na harare ta sannan nace dube ki kema xaki shiga layin masu cewa yana birge su ko kuma yana da kirki ne? tayi dry sannan tace baxa ki gane abin da ake nufi bane.momy ta matsa mishi da maganar mkrnt, hakan yasa shi nema min ta kwana gayamin yake wai shi ba xan je in hana shi sakewa da amaryanshi ba,gara in tafi ta kwana.sannan yace turkish na kaiki, in har baki tsaya kinyi krt ba Allah ba xanyi asaran kudina ba, wuya xaki sha kin sanni,kuma kika yarda kika yi wani abu na bata suna ko kibi maxan da kika iya dan akwai maxa a mkrnt saina saka bindiga na dauke ragowan nunfashinki duk mu huta,saura kuma idan momy tace kina san mkrnt kice a'a ki gamu dani.shi ke surutunshi amma ni ina maimaitawa ne a raina ina qarawa turkish ni asma'u a turkish? cab! komai yana da hanya,amma da kamban sa rai ba.momy kam tayi fadan yaya xaikai matar aure mkrnt kwana? nace nidai zanje momy inason ta Allah.momy ta yarda cikin kwana kalilan ya gama min komai yace ya aliyu ya kaini momy taki yarda ta matsa mishi saida ya bar komai ya kaaini. da duk abin da dangata yake tafiya dashi makarantar saida komai ya kammala sannan suka tafi don haushina ko sallama bai min ba, ya alyune muka yi sallama dashi na zauna bakin gado ina kallon dakin namu kato ne mai dauke da gado 4 mu 4 kenan . dakin ga kafet labulaye ga ac ga kumafankalafyayyun gadajantamkara gidan uwarkaniko gidanuwatama ban da kamar shi saurn 'yan dakin suna gurin wasanninsu domin yau lahadi duk daliban na. ga suna gurin wasanni. cangurinsha biyu da rabi saigasu sun shigo duk sa'nninane gasu masu kyau, suka bi ni da kallo nima sunake kallo,suka kalli kayana dake lode gefe daya suka kalli juna. dayar ta taso ta zauna gefena tace sannu da zuwa turkish, dyar dake can itama tazo sannu da zuwa wannan dakin namu, itako dayar gabana ta tsugunna tace shin 'yaruwa yaya sunanki? nace ni asma'u ahmad , kufa? ta gabana farar ciki itsce ta soma fadin sunana Amina turaki, mahaifina mataimaki nega shugaban kasar nan, ta gefen dama tace ni ko sunana bilkisu salis marfa, mahaifina shine ne gwamnanjigawa a yanxun ta gefen hagu tace fatima shehu, ni daya ce daga cikin jikokin shehu barno mahaifina shahararren dan kasuwane. da fatan zaki saki jikinkidamu tare da bamu goyon baya mu zama aminai,nce hakana fiso kun tabajin inda zaman makaranta yafina gida? is gurina kan na hada watana maida jikina nayi kyau red house duk muke dasu mina haka muke. kiranta tuni house captain ta zabeni a saurauniya, duk da kyawawan makarantar kokarina yasa kawayena like min, har ma da yan class ss1 n shiga lokaci guda sunana ya koma sarauniyar , duk cikin mkaranta muna da abokai maza yan class duk da bana shigemusu amma muna taimakon juna. zama da su mina yasa na goge har na manta da duk wani bacin rai,ban taba tunann akwae ranan da zatazo har inyi dariya ba, dana zata dariyata takare . ashe bahakabane, yau gashi masifataa ta dawo yanga da tsiwa duk sun dawo,dama gasu mina 'yan jan aji sai nace mana group dinmu yan jan aji mun cika girman kai. bana mantaa lokacin inter housee na yarda naci sunan queen.wayyo Allah shigar da yan red housesukayi da shirin da captain dinmu ta min zuwa farentinmu, mun burge mu nemuka zo na daya.ya aliyu da ya usman ne sukazo min su kansu sun yaba da shigar queen. mune mukazo na daya sunce min ya umar ne ya turo su dan an mishi waya ana son iyayenmu suzo muyi a gabansu, shine ya turo su, don shi suna ta shirin biki yana zarya tsakanin yola , kd da abuja sunyi kayatccen biki irin na masoya , amarya tasha kayan matsi duk dan ta hade kada ango ya gane wani ya riga shi bin hanyar. akwatina 12 dam da kaya masu tsada haka aka diba zuwa yola, a ranar jajibarin daurin aure suka shirya wani shegen lunchin kusan duk wani saurayin ta ko nace abokin shashashancintaya halarta in ka dauke alhaji sambo wanda kishi ya hana shi zuwa, kuma yace to zo suyi na ban kwana kafin nan da ta tare gidan mijinta, inko taki zaiyi yanda mijnta zai gane. haka nan duk ya daga mata hankali gurin lunchin din sai waya yake mata . ango ya damu da tambayar wake ta kiran haka? tace mutane , ta kashe wayar. da dare suna tare da sojan ta har zuwa sanda ya tafi masauki sannan ta kunna waya. alhaji sambo ya kira yace ta rufa ma kanta asiri tazo yanzu inko ba haka ba zai shirya mata tuggu, dole taje gareshi cikin wannan daren ya kwashi garar da akayi wa ango tana ji sai da safe ta dawo gida, bataso haka ba duk da yawan kudin da ya bata , haka daai ta kara wasu 'yan shirye shirye , an daura auren bayan sallah azahar kasancewar ranar asabar ce, ya umar jin shi yake yau tamkar sallah sunyi dinner katafariyar dinner da abokanshi suka c burn shirya mishi tun bara yace musu auran ya mutu su bari sai zai yi wani su al-amin manyan abokai sai yanxun suka shirya da ya umar sbd yanda yayi mishi tonon silili lokacin. auran mu, yayi ta tura wa yayita turawa abokan su na ko ina da batun auran. son ya umar lokacin ayi komai a boye .amma sai alamin ya yayi ta mishi tallata a waya wannan ya kawo musu dan sabani sai fa yanxun daya wanke kanshi gurin bingimbyafi, yayi duka d aeso boki yayi agun. sai dai farida bata kwanta mishi ba, duk kyanta nashi gurin kyawu in ya cika yawa hadari ne. *amma sai al-amin ya yayi ta mishi tallata a waya wannan ya kawo musu dan sabani sai fa yanxun daya wanke kanshi gurin bikin gimbiya , yayi duk abin da akeso aboki yayi aagun. saidai farida bata kwanta mishi ba, duk da kyanta nashi gurin kyawu inya cika yawa hadari ne.*** hafis lady ta dubi farida amarya tace in fata kin gama amfani da duk kayan da inno ta hada miki? farida tace ke dai bari,kinsan Allah , saida na gama komai dan iskan nan ahj sambo ya rusa komai, da sauri hafsi lady ta mike tana fadin amma ke farida Allah yayi 'yar iskar baiwa, yanxun dan jaraba da rashin hakuri ke da za'a kawo gidan miji sabon jini shine kikaje kika mika kanki ga wannan tsohon ya shanye duk dan tattalin da tanajin da aka ma ango? farida ta dubi aminayarta ta cikin damuwa tace wlh kawata ba da son raina bane bana ce miki yana ta damuna da waya ba? tace bana ce miki kada ki daga wayar ba? tace in ban daga damun da yakemin dole na daga, cemin yayi in har banzo munyi na bankwana ba , zai min tuggun da soja zai gane kinsan ko ba zan so haka ba. hafsi lady tace me ya hana ki kira ki sanar dani? yanda kike son soja haka yake son mulki sai kice mishi kema zaki fito ki fada ma 'yan jarida alakarku tace kash, duk tunanin baizo min ba , to yanxu na danyi amfani da wasu, tace inma ya gane ki hada da kissa da kuma kisisina, sai kice fade aka miki tun kina karama, inko bai gane ba ki share shi. farida taja filo tace aiko kin kawo shawara kawata nasan zai gane yanda yake kurin ya auri salihar mace ya sameni fanko dole hankalinshi ya tashi sukayi dariya sannan suka tafa hafsi lady tace sauaran yanda kike son shin nan ki nuna zakewarki da zalamarki zai iya ganewa, kiyi ta nokewa kina....sllamarango da abokanshi ya katse hirr tasu, nan take farida ta ja gyale ta rufe fuskarta,sun gais bayan barkwanci aka sai baki haka ango ya raka abokanshi sannan ya dawo. sun gabatar da sallar ma'aurata yayi 'yan tamboyoyi game da addini babu (not clear) dama ya zaci haka kasancewar ta kamila a nashi tunanin. soyayyarshi ya shiga nuna mata tare da wasanni tana nokewa tare da nuna tsoro hakan yasa shi binta a hamkali, yana da ilmi musamman na fikihu yasan sirrin mata da yanda halittarsu take hakan ya shiga bin komai a sannu amma sanda ya kai kofar da ya jima yana raya ma ranshi yanda zai bude ta, sai kawai yaji ta a bude, hakan ya saka jikinshi sanyi take komai ya lafa, ruf da ciki ya kwanta sai yana ji tamfar mafarki, kuka ta saka tana fadin innalillahi wa inna ilaihir raji'un dama nasan haka zata kasance a kaina, ya daure ya dube ta amma ya kasa magana, ta mike tare da neman kaya tasaka sannan ta dauki gyalenta ta rufa ta tsugunna gaban gadon inda yake kwance ka yafemin kuma Allah ya baka hakuri nasan ban caacanci ka zana dani ba ta mike zata fita yayi karfin hali ya tashi zauna a kua bakofayc z n,ta jyo fuskashi tamkar bai taba dariya ba gaban ta ya fadi. [1:56PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu1----17 Yace xonan ki gaya min dalilin bada kanki ga wani,ta soma kuka, ban bada kaina ga kowa ba, ta xauna ta daga kai tamkar mai tunani hawaye na xuba kan kumatunta,tun ina yar shekara takwas wani mlmnm bayan mun tashi mkrnt ya amshi jakata sannan ya bani wasu takardu ya ce in kai mishi su ofis.bayan na dawo yana qofar ajinmu sai yace in shiga cikin ajin in dauki jakata,ina shiga sai ya biyo ni ya rufe qofa....ta rushe da sabon kuka tankar gaske,taci gaba da fadin ya min fyade yayi kaca kaca dani ya gudu sai da aka min dinki a asibiti,ta kifaka kai tana ta kuka mai ban tausayi,uaji makira,ya taso da sauri yaxo xa rungume ta,tausayinta ne ya kika ranshi yana ji aranshi da yaga wannan tsinannan mutum babu abin da xai hana shi saka bindiga ya harbe shi,daga lallashi ya xarce soyewa,ranshi fes.duk da yaji haushin yanda ya sameta amma haka ya daure bai nuna ba tunda ba laifinta bane,soyayya suka shiga xabgawa a satin inda yaga shi qaramin dan wasane a wannan fannin itace take nuna mai salosalo na soyayya. Abin ya ta bashi mmk hr ya kai ga tambayarta a ina ta koyo wadannan salon,sanar da shi ta yi ai ma'abociyar karance-karancece, dan haka sai ya yi murna da jin haka ta mantar da shi komai. dani da ke mkrnt muka gama jarabawa a ka bamu hutu. kamar nasan ba zai zo dauka ta ba na ce Balkisu in direban ku yazo daukarki zai sa min hannu ku sauke ni kaduna.Ta ce in an zo daukarki fa? Na ce bros dina na Abujan nan ne zai zo daukata,kuma gidan shi zai kai ni ni ko ina son ganin Momy,Mina ta ce kai Queen ki tsaya a Abuja nan basa sai muna ziyartar juna ba? Na ce kin sani ne? ba ma shi da shi ne sosai zai matsa min gara in je gurin Momy haka ko direba su ya zo suka sauke ni har gida Murna gurin Momy kamar me musamman ganin yanda na koma.Sun gaisa da Balkisu sannan suka dauki hanyar jigawa ko na ce Kano,Momy ta ce me ya hana Soja yaje ya dauko ki? Na ta6e baki sannan na ce kila ya manta,ta ce wane irin ya manta? Na ce ina wayata ne? Ta ciri min ta ce gata sai kin saka a caji na ce zan kira Rahma ne ta san na dawo. Momy ta ce ina ruwan Rahma in taje gaida Mama ta kan shigo mu gaisa ai Usman ya yi sa'ar mata,na ce sosai ma ita ce dai ba ta yi sa'ar miji ba,Momy tana dry ta ce shima ai ba ruwanshi na ce ni kam gare ni ba shi da kirki,Anty ta shigo ta ce 'yan mkrnt hr kin iso? Na ce eh ina yini Anty? Muka gaisa ta ce ke da maigidan ne? Na ce a'a kawata ce suka rage min hanya,Momy ta ce shi ne zai zo ya dauko ta yana fama da Amarya? Ai zai zo ya same ni, Anty ta ce a"a Momy kin san ko bayan ta taho yaje? Ta ce ba wani zuwa da zai yi wannan kawar tata da suka kawo ta tun da daga jigawa aka je dauko ta amma na cikin Abuja bai je ba ki ce yana da niyya.Tunda nazo kaduna bai ta6a zuwa ba,Momy kuma bata neme shi ba don koda ya yi mata waya bata ta6a mishi zancena ba, Ko ta ce yaya ba muyi hutu ba? Ko kuma nazo bai zo ba sannan ta lura bai ta6a kirana ba, don haka ta ce ta san maganinshi. Abbada ya nemi ba'asin zamana a kaduna,Momy ta ce nazo ganin gida ne.Hutun mu na sati 4 ne saboda SS2 zamu shiga rannan na shiga gidanmu mun gaisa da su Mama,sai ga Rahma. Na ce yauwa kawata,dama ina ta jiranki ne kizo ki raka ni saloon,ta ce muje nima ki biya min na wanke nawa na ce lallai Momy zata ba ni sai dai kije gurin Ya Usman ko ke ma Mama ta baki? Mama ta ce zo gashi Rahma,Rahma ta fita tana dry tare da fadin wasa nake Mama,gidan su Momy shiga na yi wanka ina kwalliya muna hira da Rahma muka ji sallama gabana ne yayi wani mugun faduwa ban san mai sallamar ba,na gama na saka riga da siket na atamfa 'yar Holan mun fito falo Momy ta ce ga kudin gyaran kan na ce dari biyu ma za ki ban. Ta ce rike dari biyar din na amsa zamu fito kenan akayi sallama kofar Momy gabana ya sake faduwa ta daga labule ta shigo,Nan take na gane ta. Faridar Ya umar don bayan hotonta da na gani hr da kalandar su na gani dakin Mama hr da agogon su sanye take da wani shegen leshi wanda kyawunshi ya nuna tsananin tsadar shi. Ruwan madara ne da ratsin ja dan gyalenta shi ma ja, Haka takalmi da jaka na dauke kaina daga dubanta duk da ba son mijinta nake ba sai na ji kishinta yana yin kallon da take min tana tunanin nice matar mijinta tunda duk sauran taga su lkcn bikinta,sannan taga idon da yake ce mata yarinyae ba kyau ba,sai ido kamar na mujiya.... Ni dai muka fita kofar waje muka yi kici6is da Ya Umar ya dube ni cikin mmk ba komai ya ba shi mamaki ba yanda ya manta dani har ga Allah ya manta da wata matarshi a mkrnt yanzu mai zai ce ma Momy ban ko kuma kallon shi ba na sa kai na fita abina,Rahma ce ta tsaya gaishe shi ta biyo ni me yasa bako gaida shi ba? Na ce yanzu ba da ba ne,ba zan dauki wulakanci ba ko dama don ni sane na jur wani abina. Shi kam da ya shiga gurin Momy sai ya shiga kame-kame yana cewa shi sam mkrntr ba su mishi waya su anyi hutu ba,Aliyu ne. ya dauko ta ba shi ba ne amsar da Momy ta bashi kenan,ta fita daga dakin,Farida ta dube shi Soja na wadda tafi ta yanzu ita ce Asma'u din? ya ce eh kawai shi yasan Momy tana fushi dashi ne don ko gaisawa sama-sama suka yi ta,Ya kai Farida dakin Antynshi sanda na dawo daga saloon na gansu zasu shiga gidanmu.Yanayi tamkar ban gansu da na wuce abina,na samu Momy tana yanka Alayyahu na amshi yankan Anty Amarya tana ciki tana tuka tuwan shinkafa,dama su baka gane mai girki komai tare suke yi..... Gefen baki suka kwana da farko neman masauki ya ce zai yi a hotel,Momy ta ce duk gidan nan ko can gidan Alhj ba gurin kwana sai ka kaita hotel saboda ta raina mana arziki? To kuje sai da safe a gabn Farida ta fadi haka,nan yake ya gyara musu gefen baki tunda Aliyu baya nan haka nan su Jamila.Jamila da Nafisa suna gidan Anty Salima shi ko ya Aliyu sunyi tafiya da Abba ni dai ina can kuryar dakin Momy koma falo na zauna ba zan ta6a gyara musu gurin kwanciya ba,da safe ma sanda suka shigo na gama karyawa kawaye da Mina Turaki ina jin sanda suka yi sallama yi na yi tamkar ban san suna yi ba,Suka zauna Momy ta fita suka gaisa ya Umar sai hararata yake,na mike na shige cikin daki,ina amsa wayata,dakin Anty suka yada zango karfe 2 suka tafi bai ce ma momy komai game dani ba haka nan nima ban ce kala ba dama bana so ace in bishi Momy ma ba ta ce komai da hutun mu yana karewa ta mishi waya bai zo ba ba ya turo kudi wai Aliyu ya yi min shopping sannan yajw ya biya kudin makaranta hakan ce ta kasan ce muka koma makaranta...... Tun daga wannan ganin ban kuma ganin ya Umar ba,har muka gama SS2 muka shiga 3 duk hutu Momy zata aiko a dauke ni ta ce ma Abba ita ce na dinga zuwa kaduna saboda in an gama gini shi nan zan zauna, ko da Abba ya tuntua6e shi da wannan batun sai ya ce haka ne don haka ya saka shiriritar gama aikin nima haka na ke so, domin yanzun shi kan shi da zai ganni ba yabon kai ba yasan na fi karfin wulakanci daga shi har matarshi basa gabana na samu labarin an ce tana da ciki amma watan cikin hudu ya zube yanda nake ji gurin su Jamila tamkar zai yi kuka saboda zubewar cikin na ce su karata. Duk da matsatsin fiar da ya Umar ke ma Farida hakan bai hanata hulda da abokan shashancin ta ba,ta kan fake da zuwa gidan Yarta dake nan Abuja cikin ta ma cire shi tayi saboda yana bata matsala da abokan harkarta. Alhj Sambo shi ne ya hada ta da likitan da ya cire mata cikin. ********** cikin Yardar Ubangiji muka kammala karatunmu bayan kammala komai aka bamu kyautuka kowa ya kama gabanshi sai dai abn farin ciki ina daya daga cikin dalibai uku da makaranta ta za6a don daukar nauyinmu,muyi karatun Likita saboda hazakarmu in ka ji ana Asma'u to a kaduna ne Amma Abuja har gobe Queen suke kirana..... Sai da muka dawo gida na samu Momy zata biki jos danginta na bita muka tafi ansa bikin Hadiza da Shema'u Sai na Ya Usman da Aminiyata Rahma,Hadiza da na Ya Aliyu ne haka Shema'u yaron yayan Mamanta ne Sadik. Tun da biki ya matso ba mu da sukuni kawayena su Mina duk na gayyace sy kuma nasan za su zo. Biki ya yi biki kenan,na musu ankonmu duka don har da su cikin kawayen aana gobe daurin aure suka iso Mina tariga su isowa saboda tafi kusa,sannan Balkisu sanda Fatima shehu ta iso mun gama shirin tafiya lunchen ko hutawa bata yi ba ta yo wanka muka fito,muna ta shakiyancinmy da muka saba,Kowace direbansu ya kawo ta, don haka muka shiga motar su Mina muka shiga tunda shi direban su ya huta haka muka kayata gurin tamkar taurari gaba kin su Mina baya gajiya da fadin Queen duk in da na bi nan sauran mutune suka dauka Queen-Queen,duka amaran lunchen gurin daya muka hada tunda duk gida ne har angon shema'u tunda ya saba dama dasu ya Usman ni da Jamila mun dauki kwalayan abubuwan da zamu raba ma mutane muna kaiwa gurin ajiye wakafin mu sona rabawa,Anty Saluna ta kira ni nazo ta ce ina aurans Na ce wane aure kuma?Har ga Allah ni ina mantawa wai ni matar aure ce,Har mijin kanshi na manta da batunshi. Ta ce iye lallai Asma'u kin hadu shi yasa ko dan gyale ba ku saka ba,na ce share kin ji har zan tafi Anty Fatima ta ce kishiyarki ta ko zo? Na ce tazo bata zo ba ban sani ba,anty Aina'u ta ce na ganta gab da zamu zo nan na ce ita ta sani ni ina ruwana...... Guri ya yi guri,na rasa duk inda nayi jama'a kallona suke,ga mai wakar ya kama Asma'u Queen ban san da wanda ya sanar dashi sunana ba,Har da fadin Queen din Umar Soja marmari daga nesa,naja tsaki na ce bar hada ni da wani Soka,Jamila ta dauki kafadata ta ce dama tun dazun nake son in ce miki duk wanda ya kira ki zamu dau mataki kanshi,na ce jacan ki bani guri,yanzu nake tashena wannan Sojan ya min Tsufa,don haka duk wanda ya kira ni zuwa zanyi muka saka dariya ni da su,gashi dama muna da wata sara ni da su Mina,in munyi abin dariya mun dara sai muce wa ya dukanmu Jamila ta ce Allah ya shirye ku,Haka aka sha lunchen muka taso muna mota su Mina suka dame ni wai wanene Umar Soja? na ce don Allah ku bar zancan shi nima ban san shi ba,Fatima shehu ta ce ba wani ba ki so nw musan Saurayinki kawai Queen.Jamila zata yi Magana na toshe mata baki amma sai da ta ce musu mijinta ne,na ce kunha nayi kama da matar aure? Muna tsayawa kofar gidanmu Anty Salima ta miko min yaronta Muslim ta ce don Allah Asma'u ki kai danku gurin Momy,na ce yaron nan kato da shi yana tafiya ga surutu amma sai kuyi ta daukan shi? Ni dai ba zan dau ke ka ba sauka ka taka da kanka.Anty Aina'u ta ce dama ke ai ba ki san yara na ce ku ai yaranky sun cika kuya Anty Fatima ta ce kema in ki haifa kin rike naki na ce ba konai suka shige gidanmu mu kuma muka nufi gidan Abba da kawayena ina rike da muslim sam ban kula ba she su Ya Umar da ya Abubakr ne a gurin tare da wasu daban ban san su ba.Muslim ne naga ya kwance hannunshi ya ce ga Dadyna ya nufi gurin Ya Abubakar.Mina ta ce la ji yaro da wayi yasan Babanshi ko ba Babanshi ba ne?? Na ce Babanshi ne mana Bilkisu ta ce yayanki ne, Na ce shi ne Na farkonmu a dakin mu muka zo gota su yi nayi tamkar ban gansu su ba saboda ya Umar dake gurin sai naji su Mina suna gaishe su, har mun gota naji muryar ya Abubakar yana cewa kE Asma'u zo nan na juya na zo shi nake duba na ki kallo gurin Ya umar, na ce gani ya ce ke har yanzu..... Kanki bai dana hayaki ba ko? Na 6ata rai ya ce gaba kina kallonmu kin wani dauke kai sama sannan dubi shigarki babu ko dan gyale kin daura gwargwaro a kai gashi a waje tamkar ba matar aure ba ko?Na dubi sasheb ya Umar da gefen ido waya yake amma na kula da kallom da yake min da gefen ido, na wuce ban ce komai ba, Fatima Shehu ta ce wai da gaske kina da aure ne? Na ce don Allah muje ciki. Falon Momy na bar su na shiga dakin Anty Amarya dan na dan watsa ruwa kasancewar gidan bai cika kamar gidanmu ba,tun da nan gidan Maza ne wanka nake na tuno ya Umar da na ganshi yau in har ba zan manta ba yau shekara biyu da wata shida kenan rabona da na sa shi a idona. Ya Allah sam ban ji zuciyata tayi farin ciki da ganin shi ba,duk da cika da kyau da kwarjini da na lura ya kara,sannan ga kudi da ya zauna. Can waje kam ya Umar ya dubi Muslim sannan yasa hannu ya dauke shi tare da fadin zo nan big boy,yayi sha'awar yaron kwarai da gaske.Yanzu kam ya matsu yaga dan kanshi. Farida ya lura abin bai dame ta ba,in yayi la'akari da yanzun makarantar da ta koma tafi dauke mata hankali,ko dai zai............sai kuma yaja tsaki yayi shiru,yana son yin shawara da Anty shi ya dubi Abubakar ya ce bari na ga Antyna,Muslim ya ce zanje gurin Dadyna,ya Umar ya ce nima Dadynka ne ai ya ce a'a ga Dadyna nan Ya Umar ya mika shi suna dariya ya ce jeka gurin Babnka ya nufi cikin gidan ma ba mutune sosai kamar yanda ya zara ya shiga gefen Antynshi babu shamaki,ko ina shiga yake kai tsaye ya shige bedroom yana fadin ina Antyn tawa take? Ni kuma na fito daga ni sai wani dan tawul wanda iyakarshi cinyata,kallonaya tsya nayi wani abu ne yaji shi tub daga yatsun kafarshi har kanshi idunanshi sun kasa daukewa daga kaina. [2:07PM, 13/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu 1----18 Ganin yana min kallan qurilla na juya na koma toilet ya bini da kallo har na shige na kulle qofar. ahankali ya kulle ido ya sake bude su sannan ya jingina da bangon dakin a hankali ya furta ya salam.jikinshi babu qarfi ya fita xuwa falon anty ya xauna kan kujera wani abu yana mishi yawo aranshi yayi ajiyar xuciya tare da jingina bayanshi da kujerar,lkc guda ya kwantar da kanshi,yarinyan nan ce haka? daman haka qiranta take?wata xuciyar tace ko dai kaji sha'awanta ne?kafin ya samo amsa sai yaji maganan anty,ta dubeshi dan gidana,yayi dan murmushi ya ce ina kuka jene? tace munje kai abincin biko mana,yace kai mata kun cika bidia,yanxu tsakanin gidannan dana baba alhj har akwai wani biko ne ko bai kone ma kika ce? tayi dry tace hakama mama tace,yaja murmushi yace ina farida ne? tace aini tunda muka gaisa tace min xataje gurhn wata qawanta gashi har magariba bata dawo ba, ya ja tsaki yace tasan inta fadamin baxan barta ba shine watan ta tafi?yace anty matsaloli sunyi yawa dama ina san mu xauna.... Ya dubi agogo ga lkcn sallah yayi bari ayi isha'I cewar anty daidai nan nazo na wuce su ya dube ni sannan ya dubi anty yace yarinyar nan ta samu daurin gindi wurin momy ko gaeshe ni batayi ba . anty tace harda kai dangidana , da ace tana gidanka dole ta gaishe ka . yace bari naa dawo. mukam gidansu rahma muka nufa inda za'aje a kwashe mu xuwa zuwa gidan kanwar momy da take u/dosa , dan can xa'aa sa lalle. lkcn da ya umar ya samu xama da antynshi ya dube ta kin san anty meke damuna? na farko kamar yanda kika sani inason yara kin sani anty sannan naa 2 farida tunda ta koma makranta bataso ina mata xancen haihuwa , ga shegen yawo, look at, lkc yanxu kusan 9 bata dawo ba haka in taje makaranta bata dawowa akan lkc ga matsalar abinci saidai muci na kuku ga yawan zuwa yola suna yau suna gobe biki na gaji. anty tayi shiru a ranta tana nazarin me xatace dashi in kuma ta fad xai yarda? amma duk da haka sai tayi kuru tace umar yace naaaam tace mexai hana ka dauki matar ka asma'u ?ya dube ta da sauri tace kwrai, tana da kyau tana da diri inda bata da kunya yanxun tana dashi hakanan bata duk halayen ta daka santa dasu duk ta daina koh masifa dama sai an tabo ta, snnan zata iya haihuwa, shiru yayi yana nazarin maganar anty, ta sake dubanshi sannan kuma xakasha fama da momy . shiru yayi yana tunanin maganar anty , yasan tabbs shi bayason yarinyar saidai zata iya haihuwa amma ya zai cema momy Ya dubi anty me zance wa momy? gaskiya don son yarinyar nan banayi na tsane ta saedae don son haihuwa , xan nemi komenta ko nace zan tafi da ita saidai momy ce matsalar. dan na kula yanxun ban cikin yan harkokinta kuma duk akan yarinyar ne. anty tace ta baya xaka biyo wato wurin abba, kafin yayi magana farida ta shigo da sallama, tare da fadin anty kin ganni sai yanxun koh? ganin soja yasa tayi tsit tasan tayi laifi tun xuwan su ta kama gabanta ta zauna ta fadin danAllh kayi hkr sojana na kir wayar ka taki shiga ya dubi agogo 9 daidai sannan ya dube ta ina kikaje? kafin ta bashi amsa wayar ta tafara ruri, ta duba ta ganin ahj sambo ne yasa gabanta ya fadi, ta dauka cikin tsorofuskarta daure tace lfy? yace na kiraki ne naji kin kai gida lfy? tace eh yace kin manta pant dinki anan , tsaki taja sannan tace sai anjim, ya kwshe da dariya ta kashe wayar, yarda duk ta tsargi kanta yasa ya umar tunanin batada gaskiya, yace ina kikaje nace? nan ta soma shiryo karya , wlh wta 'yar set dinmu ce a skul dama nan suke da mijinta ke aiki can shi ne ya samar mata skul dinmu , jiya na kirata nace mun zo kd. Shine tace itama tana kdsai tamin kwatance naje. yaja tsaki yace wa kika tambaya ya baki izini ? tace yi hkr , bai kuma magana ba ya dubi anty xan tafi masaukina , don masaukin gidan nan xai cika yau.farida ta tashi bari naje ya daga mata hannu alamar kada ta bishi sannan yace inaso na samu rest of mind, ba tare da ya jira komai ba ya tafi , anty tace meyasa xkiyi gngancin nn kinsan mijinki bayason yawo? tace soja ya cika kishi ne anty, anty tace ai duk namijin da baya kishn iyalinshi jaki ne, saidai na wani yafi wani, nan suka kwanta tna tunanin yanda xata shawo kanshi dan tasan sojan bai iya fushi ba.kwance yake rigingine fuskar shi tana kallon sillntunaninshiyana kan yarnyar ,ganinta yake cikin slow tana tafiya lkcn da suka wuce da kawayenta , sannan tazo mashi rai sanda ya ganta daure da towel santla santalar cinyoyinta da kogunta ya tuna, nan zuciyarshi ta raya kwarai xata hafa mishi yara, saidai yasan xai fuskanci matsala wurin momy , ga yarinyar fa? Ranar daurin aure gidajan kam da jama'a Mu dai wannan lkcn muna gidan su Rahma Muna ta shirya yanda zamu gabatar da walima anjima bayan dauren aure.Lkcn daurin aure ya karato na ce kuzo muje gida muyo wanka kunga in gidan ya dinke da jama'a ba zamu samu gurin shiga ba,abokana ya Usman suka zo suka kawo mana drnks wanda zamu yi amfani da su gurin walima. Na ce su sauke mu gida,suka debe mu wajan har ya soma cika da mutane,gasu Ya umar da abokanshi irin su Al-Amin,da sauran su,ban da su ya Abubakar ga sunan.Muka sakko daga mota tun kan mu shiga cikin gida Mina ta dame ni da tambaya don Allah wancan yayanku ne? Mai sanye da farin boyl din can? Na dubi gurin ya Umar take magana amma sai nayi tamkar ban gane shi ba na ce wa kenan? Bilkisu ta ce wanda jiyan nan muka ganshi cikin kakin Soja, na ce sunanshi ya Umar shi ne babban yaron Momy, Fatinma shehu ta ce suna kama gaskiya,yana da kyau gayen na ce wane kyau anan? Bilkisu da Mina har suna hada baki gurin cewa ko ke ya fiki kyau Queen duk da kina mace, Na ce Allah ya kyauta,MINA ta ce yana da mata? Na ce kilama tana nan cikin gidan nan suka dage kan in tana ciki don Allah na nuna musu ita.... Tun daga nesa na hango dakin Momy fal da mutane haka falonta, haka muka ja birki kofar Anty falon ta da mutane ba su da yawa ban tsaya dubansu ba na ce ku zo nan dama kayanku na ciki.Bedroom din Anty muka shige,duk muka zube mata kan gado,na ce bari na debo mana waina ko tuwo? Suka ce wainar dai na dibo na shigo saina ga ashe harda Faridan ya Umar a cikin na zauna a falon Anty. Na shiga ina cewa kai 'yan iksa ga to matar da kuka ce in nuna maku Bilkisu ta ce matar Sojan nan? Na ce eh wata fara, duk suka tashi da gudu.Suka je suna lekenta. Suka dawo suna fadin tana da kyau gaskiya na ta6e ba ki na ce suyi ta kyansu,Fatima Shehu ta ce Amma dai ba mamnku daya ba? Nan na ce musu,nifa canne gidanmu,maman can gidan ce Mamana,ba Momy ba, yanda muke dasu yasa na basu labarin na amma ban sanar dasu yanada akayi auranmu ba na dai ce ba ma son juna aka hada mu,sun sha mamaki sannan suna ta min korafin me yasa bana sonshi dan Allah in yarda Mina cewa tayi wlh ban da ke da kike tsakani da sai na ce ina sonshi na ce ki ce mana,aini ba fa zan zauna da shi ba,ina samun wanda na ke so wlh dole ya bani sakina, Nan dai muka ci muka sha muka yi ta shakiyancin mu,sai dai kiji muna ihu muna cewa waya kwashe da dariya don ko a school in muna sama mutum iddo ya bani damu...... Wayar anty dake kan mirror ta soma kuka na duka naga ansa dan gidana nace a raina ya umar ne na aje hak yayi ta kira su mina suka ce na dauka nace a'a sojn nan ne suka ce na dai dauka don Allah tunda ta tana can cikn mutane , ina dauka ya soma fadin antyn, cikin masifa nace ba ita. bace tace to ko wcece tce frida tazo, na kshe wyar sannan nce ina ruwana da wata farida, kamar kuna ma tana gurin sai gata ta dago labule tce waye yake ambatar sunana? na mata wani duba, sannan nace to wma yasan sunanki? waya damu dake har da za'a kira sunan ki? ta zaro ido kada ki min rashin kunya don na kula da take taken ki dama baki da mutunci nace har na kai ki zaki wani zaro min ido ai ba ki fini ido ba na juya mata tawa kwayar idon. ta shigo zan faffala miki mari nima na mike ina fadin ni kuma sai na kwanta ki duke ni ko?sauran matan falon suka shigo , suna tmbayr ba'asi tace tun shigowar mu sai leqenta muke, muna mta dariya sannan yanxun har da kiran sunan ta nace ke har abin kallo ce da za'a leke ki? su minaa suna jana tace kema kinsn na fiki shiyasa da ka manna ma mijina yaki ki shiyasa kike jin haushi nace ke kin sani da inason mijinki kinyi kadan ki shigo dan dai shi kanshi bai min ba nayi wani takun tafiya da mukeyi in muna masifa nace ki dube ni da kyau, nafi Nafi karfin ajin mijinki don haka daina kishi dani ballagaza ta shigo sosai wai sai ta dake ni ,ni ko bakina baimutu ba nace koke da mijin nakikukazo zane ku ma zanyi nan dai aka fita da ita ana cewa ni yarinya ce karta kulani, su kam su bilkisu duk da sun san halina amma yau sun sha mamakina, can dai ya sukakare? oho muka sha wankanmumuka firo.anty ta kirani nazo tana tambayar me yahadamu? nace ina zuwa anty in mun dawo xan gaya miki kinsan mun tara yan walima,sai waya rahma ke bugomin, tace to a gate muka ganta ita da mijinta tana gaya mishi lkcn yan daurin aure sun watse sai dangi mun hada ido dashi na dauke kaina yi nayi tamkar ban ganshi ba, kuma karamin gyale na saka, muka shiga motar su fatima shehu da yake duk drivers da suka kawo su sunanan sai. gobe zasu tafi dasu. muna gadan har dare inda muka shiga motocin kai amaryazuwa gidan ya usmandake u/ dosa kusa dana ya abubakar , sai shirin zuwa dinner can ma mun cashe. sosai ban sanma ya umar yana gurin ba sai sanda muka zaun daga rawar da muka sha lkcn za'a fara ciye ciye , ko wani yebur mutum 4 ne, muma mu 4 ne dasu mina jamila tace bari ta samo kujera ta zauna nace a'a tace wurin su anty salima,(dama dinner din tare akayi) muna ta ciye ciye mu tare da barkwanci da muka saba.jin wani mutum nayi tsaye kusa da kaina, yace donAllah minti 1 nace wa? yace ke don Allah nace duk abin da kake son fada fadi a gabansu aminaina ne yace to don Allah sunan ki fa? in da hali kuma hour gidanku zanyi mgana fatima shehu ta rigani malam tana da miji matar aure ce na duke ta nace karya ne kaga nayi kama da matar aure? Kafin yayi magana wayata ta soma ringing cikin jaka na ciro number na gani ba suna, na duka nace hello...."muryar ya umar ta katse ni. tabbas ba kiyi kama. da matar aure ba sbd baki ba aure daraja ba, to maza ki sallame shi kafin nazo na bata muku rai dukkanku, nunawa nayi bangane mai maganar ba, nace wanene ke magana, yace zaki ganshi yanzun in baki sallami bakon ki ba ya kashe wayar. na shiga waige waige na dubi bakon nace kada ka damu bani number dinka xan kira ka nama bayan, sbd yanxun xamu wuce gida. ya ya fadamin number dinshi yace sunan shi kasimmuktar,nace sai ya jini. ya tafi su mina kallona kawai sukeyi suna mamakin yanda na tsaya sauraron wani namiji, na dinga waige wige ban ga gurin da ya umar yake ba na dubi gurin amare rahma ta min alama da hannu, wai ni ko zangamu da soja (ta nuna da alamar sarawa) nace e din, haka dinner ta ci ta cinye sannan aka kwashe mu nace gida xankoma ba zanje gidan rahma ba, saida su anty salima suka sa baki sannan mukaje washe gari budan kai ni dai tunda safe mu ka dwo sbd su mina zasu dauki hanya.kayan biki su momy mama da momyn rahma sun hada musu , ni kam momy ta bani kudi na hada musu kayan shafa suka tafi kowa ya dauki hanyar garinsu suka barni da kewa ya umar ya shigo dan sallamar su momy yana fitowa yaci karo da alhaji suka gaisa, yace dama inason shiga gurinka muyi sallama.alhaji yace madallah har zaka tafi? to ina kuma iyalin? Yace ta tafi tun jiya, yace to ita kuma wannan zaman ta kenan ko dai akwai matsala ne ? kafin yayi magana saiga motr abba, ya fito ya nufo su abba ya mika ma ahj hannu suka gais,ni kuma na fito zan shiga gidanmu, ahj yace yauwa ke zo nan, nazo gabana sai faduwa yakeyi, ahj ya dubi abba sannan yace na rasa zaman da yarinyan nan ke yi? bba yace shidin ne nima nayi magana da momynta su tace kacesi ka gama gininka na nan? ya tambayi ya umar, ya umar ya dube ni sannan yace e to , da haka nace amma yanzu na fasa bar na tafi da. ita. na dube shi da sauri sannan na dubi su abba nce ni dai donAllah ba zanje ba gaskiya yabani takar.... saukar mari naji tas, ban karasa magana ba ahj yace maza dauko kayanki ku tafi, ya umar yace a'a tabar kayan zanzo na dauka, tzo muje jin haka nayi cikin gida da gudu gurin momy ina kuka, tasaki bokitin hannunta mai dauke da ruwa, lfy asma'u? cikin kuka nake fadin su abba ne da ahj suka ce nazo nabi ya umar yanxun nan,momy tace daina kuka babu inda zakije,nayi ckin dakinta da gudu na. fada kan gado na kudondune. ina jiyo muryan abba yana fadin ina sma'un? Mu hadu a kashi na 2 don jin yanda xata kaya, domin akwai lbr. Insha Allah zan kare daga na 2 na gode Taku HALIMA ABDULLAHI K/MASHI. [7:20PM, 17/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu 1----18 Ganin yana min kallan qurilla na juya na koma toilet ya bini da kallo har na shige na kulle qofar. ahankali ya kulle ido ya sake bude su sannan ya jingina da bangon dakin a hankali ya furta ya salam.jikinshi babu qarfi ya fita xuwa falon anty ya xauna kan kujera wani abu yana mishi yawo aranshi yayi ajiyar xuciya tare da jingina bayanshi da kujerar,lkc guda ya kwantar da kanshi,yarinyan nan ce haka? daman haka qiranta take?wata xuciyar tace ko dai kaji sha'awanta ne?kafin ya samo amsa sai yaji maganan anty,ta dubeshi dan gidana,yayi dan murmushi ya ce ina kuka jene? tace munje kai abincin biko mana,yace kai mata kun cika bidia,yanxu tsakanin gidannan dana baba alhj har akwai wani biko ne ko bai kone ma kika ce? tayi dry tace hakama mama tace,yaja murmushi yace ina farida ne? tace aini tunda muka gaisa tace min xataje gurhn wata qawanta gashi har magariba bata dawo ba, ya ja tsaki yace tasan inta fadamin baxan barta ba shine watan ta tafi?yace anty matsaloli sunyi yawa dama ina san mu xauna.... Ya dubi agogo ga lkcn sallah yayi bari ayi isha'I cewar anty daidai nan nazo na wuce su ya dube ni sannan ya dubi anty yace yarinyar nan ta samu daurin gindi wurin momy ko gaeshe ni batayi ba . anty tace harda kai dangidana , da ace tana gidanka dole ta gaishe ka . yace bari naa dawo. mukam gidansu rahma muka nufa inda za'aje a kwashe mu xuwa zuwa gidan kanwar momy da take u/dosa , dan can xa'aa sa lalle. lkcn da ya umar ya samu xama da antynshi ya dube ta kin san anty meke damuna? na farko kamar yanda kika sani inason yara kin sani anty sannan naa 2 farida tunda ta koma makranta bataso ina mata xancen haihuwa , ga shegen yawo, look at, lkc yanxu kusan 9 bata dawo ba haka in taje makaranta bata dawowa akan lkc ga matsalar abinci saidai muci na kuku ga yawan zuwa yola suna yau suna gobe biki na gaji. anty tayi shiru a ranta tana nazarin me xatace dashi in kuma ta fad xai yarda? amma duk da haka sai tayi kuru tace umar yace naaaam tace mexai hana ka dauki matar ka asma'u ?ya dube ta da sauri tace kwrai, tana da kyau tana da diri inda bata da kunya yanxun tana dashi hakanan bata duk halayen ta daka santa dasu duk ta daina koh masifa dama sai an tabo ta, snnan zata iya haihuwa, shiru yayi yana nazarin maganar anty, ta sake dubanshi sannan kuma xakasha fama da momy . shiru yayi yana tunanin maganar anty , yasan tabbs shi bayason yarinyar saidai zata iya haihuwa amma ya zai cema momy Ya dubi anty me zance wa momy? gaskiya don son yarinyar nan banayi na tsane ta saedae don son haihuwa , xan nemi komenta ko nace zan tafi da ita saidai momy ce matsalar. dan na kula yanxun ban cikin yan harkokinta kuma duk akan yarinyar ne. anty tace ta baya xaka biyo wato wurin abba, kafin yayi magana farida ta shigo da sallama, tare da fadin anty kin ganni sai yanxun koh? ganin soja yasa tayi tsit tasan tayi laifi tun xuwan su ta kama gabanta ta zauna ta fadin danAllh kayi hkr sojana na kir wayar ka taki shiga ya dubi agogo 9 daidai sannan ya dube ta ina kikaje? kafin ta bashi amsa wayar ta tafara ruri, ta duba ta ganin ahj sambo ne yasa gabanta ya fadi, ta dauka cikin tsorofuskarta daure tace lfy? yace na kiraki ne naji kin kai gida lfy? tace eh yace kin manta pant dinki anan , tsaki taja sannan tace sai anjim, ya kwshe da dariya ta kashe wayar, yarda duk ta tsargi kanta yasa ya umar tunanin batada gaskiya, yace ina kikaje nace? nan ta soma shiryo karya , wlh wta 'yar set dinmu ce a skul dama nan suke da mijinta ke aiki can shi ne ya samar mata skul dinmu , jiya na kirata nace mun zo kd. Shine tace itama tana kdsai tamin kwatance naje. yaja tsaki yace wa kika tambaya ya baki izini ? tace yi hkr , bai kuma magana ba ya dubi anty xan tafi masaukina , don masaukin gidan nan xai cika yau.farida ta tashi bari naje ya daga mata hannu alamar kada ta bishi sannan yace inaso na samu rest of mind, ba tare da ya jira komai ba ya tafi , anty tace meyasa xkiyi gngancin nn kinsan mijinki bayason yawo? tace soja ya cika kishi ne anty, anty tace ai duk namijin da baya kishn iyalinshi jaki ne, saidai na wani yafi wani, nan suka kwanta tna tunanin yanda xata shawo kanshi dan tasan sojan bai iya fushi ba.kwance yake rigingine fuskar shi tana kallon sillntunaninshiyana kan yarnyar ,ganinta yake cikin slow tana tafiya lkcn da suka wuce da kawayenta , sannan tazo mashi rai sanda ya ganta daure da towel santla santalar cinyoyinta da kogunta ya tuna, nan zuciyarshi ta raya kwarai xata hafa mishi yara, saidai yasan xai fuskanci matsala wurin momy , ga yarinyar fa? Ranar daurin aure gidajan kam da jama'a Mu dai wannan lkcn muna gidan su Rahma Muna ta shirya yanda zamu gabatar da walima anjima bayan dauren aure.Lkcn daurin aure ya karato na ce kuzo muje gida muyo wanka kunga in gidan ya dinke da jama'a ba zamu samu gurin shiga ba,abokana ya Usman suka zo suka kawo mana drnks wanda zamu yi amfani da su gurin walima. Na ce su sauke mu gida,suka debe mu wajan har ya soma cika da mutane,gasu Ya umar da abokanshi irin su Al-Amin,da sauran su,ban da su ya Abubakar ga sunan.Muka sakko daga mota tun kan mu shiga cikin gida Mina ta dame ni da tambaya don Allah wancan yayanku ne? Mai sanye da farin boyl din can? Na dubi gurin ya Umar take magana amma sai nayi tamkar ban gane shi ba na ce wa kenan? Bilkisu ta ce wanda jiyan nan muka ganshi cikin kakin Soja, na ce sunanshi ya Umar shi ne babban yaron Momy, Fatinma shehu ta ce suna kama gaskiya,yana da kyau gayen na ce wane kyau anan? Bilkisu da Mina har suna hada baki gurin cewa ko ke ya fiki kyau Queen duk da kina mace, Na ce Allah ya kyauta,MINA ta ce yana da mata? Na ce kilama tana nan cikin gidan nan suka dage kan in tana ciki don Allah na nuna musu ita.... Tun daga nesa na hango dakin Momy fal da mutane haka falonta, haka muka ja birki kofar Anty falon ta da mutane ba su da yawa ban tsaya dubansu ba na ce ku zo nan dama kayanku na ciki.Bedroom din Anty muka shige,duk muka zube mata kan gado,na ce bari na debo mana waina ko tuwo? Suka ce wainar dai na dibo na shigo saina ga ashe harda Faridan ya Umar a cikin na zauna a falon Anty. Na shiga ina cewa kai 'yan iksa ga to matar da kuka ce in nuna maku Bilkisu ta ce matar Sojan nan? Na ce eh wata fara, duk suka tashi da gudu.Suka je suna lekenta. Suka dawo suna fadin tana da kyau gaskiya na ta6e ba ki na ce suyi ta kyansu,Fatima Shehu ta ce Amma dai ba mamnku daya ba? Nan na ce musu,nifa canne gidanmu,maman can gidan ce Mamana,ba Momy ba, yanda muke dasu yasa na basu labarin na amma ban sanar dasu yanada akayi auranmu ba na dai ce ba ma son juna aka hada mu,sun sha mamaki sannan suna ta min korafin me yasa bana sonshi dan Allah in yarda Mina cewa tayi wlh ban da ke da kike tsakani da sai na ce ina sonshi na ce ki ce mana,aini ba fa zan zauna da shi ba,ina samun wanda na ke so wlh dole ya bani sakina, Nan dai muka ci muka sha muka yi ta shakiyancin mu,sai dai kiji muna ihu muna cewa waya kwashe da dariya don ko a school in muna sama mutum iddo ya bani damu...... Wayar anty dake kan mirror ta soma kuka na duka naga ansa dan gidana nace a raina ya umar ne na aje hak yayi ta kira su mina suka ce na dauka nace a'a sojn nan ne suka ce na dai dauka don Allah tunda ta tana can cikn mutane , ina dauka ya soma fadin antyn, cikin masifa nace ba ita. bace tace to ko wcece tce frida tazo, na kshe wyar sannan nce ina ruwana da wata farida, kamar kuna ma tana gurin sai gata ta dago labule tce waye yake ambatar sunana? na mata wani duba, sannan nace to wma yasan sunanki? waya damu dake har da za'a kira sunan ki? ta zaro ido kada ki min rashin kunya don na kula da take taken ki dama baki da mutunci nace har na kai ki zaki wani zaro min ido ai ba ki fini ido ba na juya mata tawa kwayar idon. ta shigo zan faffala miki mari nima na mike ina fadin ni kuma sai na kwanta ki duke ni ko?sauran matan falon suka shigo , suna tmbayr ba'asi tace tun shigowar mu sai leqenta muke, muna mta dariya sannan yanxun har da kiran sunan ta nace ke har abin kallo ce da za'a leke ki? su minaa suna jana tace kema kinsn na fiki shiyasa da ka manna ma mijina yaki ki shiyasa kike jin haushi nace ke kin sani da inason mijinki kinyi kadan ki shigo dan dai shi kanshi bai min ba nayi wani takun tafiya da mukeyi in muna masifa nace ki dube ni da kyau, nafi Nafi karfin ajin mijinki don haka daina kishi dani ballagaza ta shigo sosai wai sai ta dake ni ,ni ko bakina baimutu ba nace koke da mijin nakikukazo zane ku ma zanyi nan dai aka fita da ita ana cewa ni yarinya ce karta kulani, su kam su bilkisu duk da sun san halina amma yau sun sha mamakina, can dai ya sukakare? oho muka sha wankanmumuka firo.anty ta kirani nazo tana tambayar me yahadamu? nace ina zuwa anty in mun dawo xan gaya miki kinsan mun tara yan walima,sai waya rahma ke bugomin, tace to a gate muka ganta ita da mijinta tana gaya mishi lkcn yan daurin aure sun watse sai dangi mun hada ido dashi na dauke kaina yi nayi tamkar ban ganshi ba, kuma karamin gyale na saka, muka shiga motar su fatima shehu da yake duk drivers da suka kawo su sunanan sai. gobe zasu tafi dasu. muna gadan har dare inda muka shiga motocin kai amaryazuwa gidan ya usmandake u/ dosa kusa dana ya abubakar , sai shirin zuwa dinner can ma mun cashe. sosai ban sanma ya umar yana gurin ba sai sanda muka zaun daga rawar da muka sha lkcn za'a fara ciye ciye , ko wani yebur mutum 4 ne, muma mu 4 ne dasu mina jamila tace bari ta samo kujera ta zauna nace a'a tace wurin su anty salima,(dama dinner din tare akayi) muna ta ciye ciye mu tare da barkwanci da muka saba.jin wani mutum nayi tsaye kusa da kaina, yace donAllah minti 1 nace wa? yace ke don Allah nace duk abin da kake son fada fadi a gabansu aminaina ne yace to don Allah sunan ki fa? in da hali kuma hour gidanku zanyi mgana fatima shehu ta rigani malam tana da miji matar aure ce na duke ta nace karya ne kaga nayi kama da matar aure? Kafin yayi magana wayata ta soma ringing cikin jaka na ciro number na gani ba suna, na duka nace hello...."muryar ya umar ta katse ni. tabbas ba kiyi kama. da matar aure ba sbd baki ba aure daraja ba, to maza ki sallame shi kafin nazo na bata muku rai dukkanku, nunawa nayi bangane mai maganar ba, nace wanene ke magana, yace zaki ganshi yanzun in baki sallami bakon ki ba ya kashe wayar. na shiga waige waige na dubi bakon nace kada ka damu bani number dinka xan kira ka nama bayan, sbd yanxun xamu wuce gida. ya ya fadamin number dinshi yace sunan shi kasimmuktar,nace sai ya jini. ya tafi su mina kallona kawai sukeyi suna mamakin yanda na tsaya sauraron wani namiji, na dinga waige wige ban ga gurin da ya umar yake ba na dubi gurin amare rahma ta min alama da hannu, wai ni ko zangamu da soja (ta nuna da alamar sarawa) nace e din, haka dinner ta ci ta cinye sannan aka kwashe mu nace gida xankoma ba zanje gidan rahma ba, saida su anty salima suka sa baki sannan mukaje washe gari budan kai ni dai tunda safe mu ka dwo sbd su mina zasu dauki hanya.kayan biki su momy mama da momyn rahma sun hada musu , ni kam momy ta bani kudi na hada musu kayan shafa suka tafi kowa ya dauki hanyar garinsu suka barni da kewa ya umar ya shigo dan sallamar su momy yana fitowa yaci karo da alhaji suka gaisa, yace dama inason shiga gurinka muyi sallama.alhaji yace madallah har zaka tafi? to ina kuma iyalin? Yace ta tafi tun jiya, yace to ita kuma wannan zaman ta kenan ko dai akwai matsala ne ? kafin yayi magana saiga motr abba, ya fito ya nufo su abba ya mika ma ahj hannu suka gais,ni kuma na fito zan shiga gidanmu, ahj yace yauwa ke zo nan, nazo gabana sai faduwa yakeyi, ahj ya dubi abba sannan yace na rasa zaman da yarinyan nan ke yi? bba yace shidin ne nima nayi magana da momynta su tace kacesi ka gama gininka na nan? ya tambayi ya umar, ya umar ya dube ni sannan yace e to , da haka nace amma yanzu na fasa bar na tafi da. ita. na dube shi da sauri sannan na dubi su abba nce ni dai donAllah ba zanje ba gaskiya yabani takar.... saukar mari naji tas, ban karasa magana ba ahj yace maza dauko kayanki ku tafi, ya umar yace a'a tabar kayan zanzo na dauka, tzo muje jin haka nayi cikin gida da gudu gurin momy ina kuka, tasaki bokitin hannunta mai dauke da ruwa, lfy asma'u? cikin kuka nake fadin su abba ne da ahj suka ce nazo nabi ya umar yanxun nan,momy tace daina kuka babu inda zakije,nayi ckin dakinta da gudu na. fada kan gado na kudondune. ina jiyo muryan abba yana fadin ina sma'un? Mu hadu a kashi na 2 don jin yanda xata kaya, domin akwai lbr. Insha Allah zan kare daga na 2 na gode Taku HALIMA ABDULLAHI K/MASHI. [7:25PM, 17/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: FUSKA BIYU PART 2 NA HALIMA ABDULLAHI K/MASHI Fuska Biyu2----1 Ya dubi agogo shida agogon ya nuna yanzu ta cika. Daidai sannan farida ta turo kofa ta shigo tare da sallama. Jikinta sanye cikin dogon hijjabi mai hannu.hijjabin ya sauka har kasa don ya rufe takalminta. Ya umar ya dube ta cikin sakin fuska. Har ga Allah yana kara son farida sbd kamewar da ke gareta. Itama cikin kulawa ta iso gare shita dube shi ta ce "yau ka riga ni dawowa sojana, wlh wani leacturer ne bai shigo ba sai to 5,inata sauri don nasan baka son ka dawo bana gda "ya ce, "kada ki damu, tace ina zuwa baki ta shiga wata bedroom dinta cikin sauri ta cire kayan jikinta don tasan zaya iya biyo ta dakin jis ne da wata yar riga mai kama da singileti sai ta dora after dress kan su sannan tasa wannan hijabin. Tana isa makaranta ta cire hijabin cikin mota ta barshi sai fa da ta gama gantalinta da malamai sannan tasa ta dawo gda. Atamfa ta saka riga da zani ta fito falon gurin frigde ta nufa maltina ta ciro na gwangwani masu shegen sanyi ta nufi gurinshi,ta balle hancin gwangwanin ta mika bakinshi, ta kama gwangwanin tare da hannunta kanciyarshi yayi mata masauki,ta zaba mishi maltina cikin bakin shi,ya sha yayi ajiyar zuciya ya dube ta."shi yasa nake kara sonki farida domin kinsan abun da nakeso da kuma wanda banaso burina shine ing dan mu ko 'yar mu ke yara ma da yawa son samu" ta dan dube shi " nima nawa burin kenan,amma lokaci ne" yace ga shawara ta dube shi da sauri ta me fa? Ya kara janta jikinshi me zai hana muje muga dokto? Gabanta ya fadi lallai in har ta bari suka je gurin dokto asirita zai tonu domin Alhaji Sambo yasa an daure mata mahaifa ya umar ya katse mata tunani kinyi shiru my farida, nan take ta dawo nutsuwarta. Duk da tna cikin rudu ta daure tace ka gane ne? Ita rayuwa komai saika yi hakuri kada ka damu tunda ka taba mun ciki nida kai duk mun san muna haihuwa. Sannan in mun ce sai munje an duba mu wannan yiwa Allah shisshigi ne tamkar mun raina baiwar lafiya kyau da kuma arzikin da ya mana ne in ko mun yi hakuri sai ya bamu ta in da ba ma zato Don haka mu dogara gare shi ta dubi fuskarshi da alama maganar ta soma tasiri gareshi a ranta tace danne ma tunda kai sai ance Allah sannan zaka yadda haka zanta bi ina shigar da kai ta ci gaba, ka duba wani ba kudin ba lafiya sannan bbu haihuwa, wani kuma a bashi haihuwar amma bashi da abun da zai koda ci da su. Ta rugume shi kayi hakuri sojana mai nema yana tare da samu ,nasan Allah bazai barka haka ba yanda ta kasance mai taka tsan-tsan doki kai shi lokacin ne yace ngd farida duk zantukanki haka ne Allah zai kawo lokaci nga. Ya mike don zuwa masallaci, yayin da farida ta fada daki ta haye gado tana kwasar dariya. Layin Alh. Sambo ta kira tana sheka dariya sunan da ta saka mishi Hajiya Sabuwa haka ta ke yi duk lambobin maza abokan harkarta sai ta saka sunan mata sbd kada sojanta ya gani dama baya daukar wayarta sbd zaton shi duk mata ne Ta kira Alh. Sambo tan bashi lbrn ynda suka yi yanzun da sojanta shima dariyar yake yi tare da fadin sakarai shi zatomshi wata malama ce ke ta ce kyale shi yaushe zan tasya ga kyautar shida bata wuce dubu dari. Alhajina gaku masu kyautar miliyon. Babanmu yayi min waya ya ce in maka godiya ka canza masa mota ko? Yace a'a yafi karfin haka gare ni tace mun gode sai anjima firgigit! ya umar ya farka daga mummunan mafarkin nashi, yayi shiru xuciyarshi kuma tana maimaita mishi ddu'oi, zufa ce yayi tamkar wanda yayi wanka , ya dubi farida dake shara bacci, ya som tuno mafarkinshi. farida ce da wuka take binshi xata sara mishi ya gudu tan bin shi har ya fadi tazo zata luma mashi, sai ga yarinyar nan da zai iya tuna sunan ta wacce aka aura mishi tazo ta fisge t luma ma faridan, sannan ta kama hannunshi sukanufi wani lambu,sai waigen faridar yakeyi yana mamakinta a ranshi yana cewa , laillai makashinka yana gindin ka, sai wannan yarinya ta nuna mshi wasu kyawawan yara ta xe kaga yarnka can, gudu ya soma dan xuwa gare su, amma sai gurin yayi mishi nisa tun karfinshi yake gudu amma har ya gaji bai kai banan ya farka firgigit.shikamba shi da ilimin sanin fassara mafarki don haka sai ya barshi a cewa rudi ne irinna shaidan, in ma da wani abu ya bar ma ubangiji damashine mafi sani, sannan ya tashi yayo alwala dan yin nafila, ubangijin talkai ya shiga kai ma kuka tsawon lokaciyana ibada kafin dagabasani ya koma makwancinsa , kasa rintsawa yayi cikin tunanin ya nutsa gaskiya zuciyarshi tana matukar son yara yaso yazo da yarinyarnankilaitace keda rabon haihuwa ma a tare da shi, duk da iya bakin kokari ranar da zai dawo yayi donmomy ta yarda ya taho da ita amma momy taki duk da bkin da abba yasa,amma tunda sunce zasuneme shi zai jira, shi ba wai yana sonta bane yana dai saka rai zata haifa mishi yara ne, in ma yana gudun kada ta musu muguwar tarbiya sai ya ba farida tayi musu tarbiya irin ta addinin musulunci. addua yayi ya rumtse ido har bacci ya dauke shi niko tun ranr dasu alhaji sukace in bi ya umar duk sai hankalina ya tshi an dan so a kai ruwa rana da abba da momy sbd tace lallai ba inda zanje. yanxun ne yasn danin ahj ma y shigo sukace lallai na fito na boye momy tace ba xanje ba, ya umar daya shigo dan tararshi tayi gami da cewa yayi maza ya bace mata da gani jinhaka yasa yace su tafi abba yace kaje zamu kira ka suk fita.fushi sosai abba ya dauka da momy cikin kwanan kin zaton su momy ce ke zugani, ita ko lallashna take in yarda in koma zata mishi fadanshare ni da yayi, domin in 'yarta aka ma hakaba zata so ba.cikin kuka nace momy ni wlh dan yakikulani b shi bane damuwat ba, ya umar ya ganamin azaba a zamanmuna kudu, nan na kwashe komai na gaya mata. shiru tayi tana kallona, can ta numfasa sannantace , hakika yayi kuskure kuma xan nuna mishi kuransa, yanxun in sun matsa sai kin tafi tokije amma kafin ki tafin zaki kunyarshi, sannan zan ba ki kudin mota dakin gayaya ki taho gaa kuma waya xan dinga kiranki ina jin halin da kike ciki? kuka na ska ina cewa ni dai Allah mony kiyi hakuri ba zanje ba, ta lallashe ni da cewa to kiyi shiru shi kenan kiyi xamanki nan in ya gama ginin shi na nan kd sai ki koma, shiru dai nayi amma dana koma gidan ya umar ai gara na shiga uwa duniya. abba da ahj kullum mitin suna magana kan nida ya umar ban san me suke tattaunawa ba,har kwana5. cikin kwanakin na kula da rshin shirin dake tsakaninabba da momy, haka baya min dadi sam,ranar kwana 5 da maganar tun a safe ina kudundune cikin bargo sbd sanyin da ske tsulawa . jamila ta shigo dakin momy inda nike kwance tace kizo asma'u su abba suna kiranki a falo nace to, tashi nayi na nufi falon abba , duk da barin da jikina yake yi. kamar yanda na zatashi da ahj na same su zaune duk fuskokinsu babu annuri. ahj ne ya soma mgn tunda bazaki gaishe mu ba, to dama ba ita muk akira kiyi mana ba, da saurinace ina kwananku? ahj ya kara katse nikirike abinki,mun kira kine mu shaida miki ki shirya gobe juma'a mijinki zaizo ku tafi,na soma kuka ina cewa don Allah kuyi hkr wlh ya umar baya kaunar ganina, ahj ya taso xai dake ni, abba ya rikeshi kadaka dake ta ba lafin tabane ita momy dinta su ai itace ta daure mata gindi, don haka kabr ta itama momy din tasu auranta yana rawa. da saurina daga kaina dubi abba,nace Allah abba ba ruwan momy, ahj yakatseniki shiga shirin komawa gobesbd mune muka haife kibakecekika haife mu ba,wannan cemgn bama son jin komai daga gare ki,na tashi ina kuka ban kai ga fitowa ba naji sallamar mama,na tsorata sbd tun da nakea gidan nan zan iya cewa zuwnmama baifi sau 3 ba, sumasai da dalili, yau km nasan zuwanane tunda ga rigamr da akeyi, na fito da sauri ta dube ni sannan tace yayi mikikyau, wannan rashin mutuncin da kika iya shi zaki mana yanxunko? to bari kijii in har baza ki koma gidan mijin kiba,babu ni babu ke,sannan ma ta aje ki ta kula dake ke kuma zaki rabata da danta da kumaauranta,to maza kihada kayankiance gobezaizo inyazoki bishi in kuma kinki to ki nemi gidan uban da zakijeba zaki zaunaki kashe mata aure ba, shibai guje ki ba kace mai gudunsa? sakarya shashasha, mara tunani, ta juya ta fita nabi ta da kallo a raina ina raya wato daini kullum. cikin lafi nake? kila mahaka zan koma ga ubangijina cikin bakin ciki Allah ka dubeni na. shiga dakin momytna zaune tayi tagumi nasan taji duk abin da mama tace na zube a jiknta ina. kuka. lallashi na ta shiga yi tare dacewa, in yarda in koma, in naga abin da bai min ba toinkira ta zata zo tataho dani ka dama nazo a galaifina,nace shikenan zanje, tace shima zaizo ya sameni duk yinin ranar lallashinamomy keyi, anty amarya kuma ake har hada minkaya, ga wasu abubuwa damomy tayi ta bani ina sha harda su na wanka da sauransu. washe gari tun goma an gama shirya minkayana tsaf naje salon suka wanke min gashi naso zuwa gurin rahma amm ba dama, domin momy tamin waya wai nayi sauri,ashe ya isone dan ina zuwa kofar gida na ga motarshi, sandana shiga dakn momy na same ta sai mishi fada takeyi, banda hakuri babu abin da yake bata, na shiga tace gata nan ta bika amma nace daka muzguna mata to ta tahoko tayomin waya nazo na dauketa. suko su abba fada suka min tare da jan kunne ko gidanmu ban shiga ba muka dauki hanya duk ni dashi bayan mota muka zauna, wani soja ke janmu cikin wata galleliyarhenesi, tunda muka shiga fuskarshi a turbune tamkar anaiko mishi da sakonmutuwa, nace a raina kataras, zan baka mamaki wannan karon ba waccan asma'u daka sani bace, ba wadda ka gasa bace wannan saedae ta gasaka, na bude jakata na ciro cingam na bre na jefabaki naci gaba da tauna, sannan na ciro waytana shiga neman layin rahma, tadauka nace amarya kin sha kamshi, tace dole ne kice nasha kamshi bakinki zuwa kema na dan sammiki kamshinba?nace ke naso zuwa amma yanxun ba rana dangani bisa hanyarabuja, tace haba nace wlh,tace skul? nace a'a su ahj sun koreni in na cemakiba'a sonakice karyane,tace gidan ya umar?nace sai. kiyikuma, kadaki cinye min kudi anjimakikirani gara ke kina da mai saka miki sai na jiki tace shi kenan sai kin jini. na aje wayar a kan cinyata, na bude volume dinta na kira mina tace sai yau kika kirani? Nace sorry mina bana cikn nutsuwa ne 2days, shiyasa ko. su fatima ma bankira suba.ina ga yau zan shigo abujanku, tace to queen sai naji kiran ki bye. haka nan na kira fatima da bilkisu duk nayi musu bangajiyan biki, yana jinana jefa wayata cikin aljihun jaka na jingina, can aka kira shi ya dauka naji yace, my farida kin dawo gida ne? ban san amsar da taba shi ba, sai naji yace ok, tonima hani nan bisa hanya kisa su joseph su share BQ dinnan muna xuwa yanxun da bakuwa, na dube shida sauri waton ni xa'a saka a BQ, zaka sha mamaki, na raya a raina. kowace amsa ta bashi?sai naji yace yarinyar nance, eh ita ya sake yin shiru,tana ta mgn ba dai najin ko me take fada sai naji yace,o no kada ki damu, kin san ba zanja da mgnr su abba ba shine kawai ban da su da ke tsakani mexanyi da ita?ka dama ki damu. a raina nace, yau za'ayi ta donnima din wlh ba zan dauk rainin hankali ba. muna isa wani mahaukacin gida muka shiga acikin abacha barak, na kula gurin duk manyan sojoji ne donhaka tunfarkon unguwar har gidan da mukaje sojoji ne, daya gama parking muka fito yasa wasusojoji suka kwashi kayana zuwa BQ dan sunce mishi sun gyara,yace min na bisu,ban musa ba donkada na ba da shi naga sai wani famankame mishi sukeyi, muna shiga naga wani madaidaicin falo mai dauke da setin kujeru,duk sun kode yadinsu naga dakunanbacci 2 na leka duka da gadaje kanana sai kicin da bayi a duk cikin falon ban zauna nan ba ai ni ba 'yar aikinshi bace,nan na fita na bar kayan nan cikin falon na nufi ainihin gidan nasu,tafiya ce mai shegen nisa,kafin akai cikin gidan,a raina nace haka kawa ba zan zauna ba cikin bishiyoyiba salon maciji ya sare ni, na shiga falonsu ko sallama ban y ba, farida nagani tana shirya abinci kandiin ta ta kalloni taga inda zanje na samu kujera na hakimce ina kallon TV, tabar abin da takeyi ta nufi wani daki ina ganin nan ne dakin shi . Jim kadan sai gasu tare ya cire kaki jallabiya ce fara tas a jikinshi, sai gilas dinda nike zaton na kara karfin ido ne don koda yaushe yana idon shi, yazo warin da nake fuska tamke yace me kikazo yi nan? Na mishi wani duba sannan nace kai zan tambaya na maida idona ga kallon TV yace ke bari kiji baza kizo ki dama min lissafi ba dan in da nasa aka raka ki can ne mazauninki, nace tabdijam wallahi ba zan zauna a can ba kuma ba yar aikinku bace ni, ya daka min tsawa ke yimin shiru mara kunya wuce ki koma, na gyara zama nace nifa babu inda zanje. Farida ta dube shi, sojana gaskiya yarinyan nan bata da kunya, ya daka min tsawa ba zaki tashi ba? Nayi banza dasu na daura kafa daya kan daya, na ciro wayata na soma kiran layin momy, ya tsargu zan kira momy ne sai yace farida jeki ci gaba da aikinki, nace momy mun iso, tace kun iso lfy? Nace lfy lau, sai dai kan in karasa ya amshe wayar, na dube shi nace bani wayata don ba kai ka saimin ba, ya soma fadin rufe min baki ko in zane ki yanzun nan kina jina ko? Nima na mike nace kai Nima na miqe nace kai damisar takarda, ka sani na daina tsoranka yanxu, da ka buga amma yanxu mai dukana sai ruwan sama wlh, kallona yakeyi na sani yana mamakin canxawar dana yine, dama araina nace haukan tsiya xan musu. komawa dakin matarsa yayi, taxo ta dubeni qaryan rashin kunxa kike yi baxaki xauna min gidana ba, na miqe na mata kallan banxa nace gidan banxa da wofi gareki? to inasan ki sani da gidanki da mijinki duk basa gabana,ni da xaki taimaka min kisashi ya rbt min takarda,domin baya cikin maxajan dana keso, ki daina kishi basan mijinki nake yi ba,yanxuma ya baki lbrn yanda akayi na yarda na biyo shi, tace ai shima ba sanki yake yi ba,me xaiyi da karuwa? na dube ta da sauri waye karuwa?tace ke,mai yawon hotel.. ***************** [7:26PM, 17/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu 2----2 Tace ai shima ba sanki yake yi ba,me xaiyi da karuwa? na dube ta da sauri waye karuwa?tace ke,mai yawon hotel.. Takaici yaxo min kenan gun mijinta taji? haushi daya kamani nace ni da uwarki muke xuwa hotel din ko? ta nufo ni wai xata dake ni, nace taba ni ki gani .hayaniyarmu ta fito dashi yaxo ya ja matarsa tana fisgewa wai saita duke ni suka tafi, na koma kan kujera na xauna na ce wannan karan baxan dauki raini ba, insha Allah haka xan gallabe ku har ya gaji ya maidani inda ya daukoni, suna shiga daki tasa masa kukan kissa tana fadin nidai wlh saidai ka xaba koni ko ita,ji yanda take xaganmin uwa, ya jawota jikinshi ya rungume tare da cewa come on my farida, ina san ki gane ita yarinyan nan tana taqama dane da momy,so take tayi sanadin da momy xatayi fushi dani,kinsan kuma bana san bacin ran iyayena shi yasa takeyin wannan abin,tanasan na kulata ta samu dama ta hadani da momy,kin gane? ta daga kai yace ta pls ki barta ta xauna cikin wancan dakin da babu kowa, sannan kome xata yi kada ki kulata in naxo dai ki gayamin, kuma irin neman fadanta xan raba maku kwana,da sauri farida ta dubeshi yace kin ganf? Bawai xan kwana da ita bane, a'a ranar girkinta sai ki kwana dakinki ni kuma na kwana a nawa,tace me yasa sojana? yace xata iya cewa an tauye mata haqqinta, tace amma fa kada kayi amfani da ita taje ta raina min wayo, sannan gaskiya inma kaje gunta saidai ka nemi wata matar dan ina qyamar namiji yaje gun wata sannan yaxo guna, yace dan wannan kada ki damu amma a cikin ranshi mamakinta yake ji,da wani abinne da yanxu xata soma cewa Allah yace annabi yace, matsayinsa na mai ilimi ya sani yarinyan tana da haqqi kanshi tun lkcn da aka daura musu aure,shi kam xai nemeta dan yana ji a jikinsa xata haifa masa yaya shi kanshi bai sam dalilin shi na kasa yi mata hukunci kan abinda tayi ba,amma yasan abin yi in tana taqama da momy ne, xai dafata cikin ruwan sanyi.ya dubeta kada ki damu dan wannan ni naki ne ke kadah kin gane?ta daga kai alaman eh, ya fito yaxo inda nake fuskarshi tamke,nima haka ya rame ni nayi banxa dashi ya sake cewa kina jina ko? naki dubanshi yace ko baki kalleni ba nasani kunene ke ji. Yaci gaba ga daki can ki debo kayanki ki dawo bana san wannan complen din, na dube shi sannan na dubi gun da nake xaton dakin na tashi nace to dama dama dai, na nufi dakin,ba uwar komai daga katifa sai wardrop da toilet nace gara nan nida banxo xama ba mexan yi da wani daki,na fito dan qarfin hali irin nawa gun sojojin nan naje nace ogan su yace su kwoso kayan da suka kai BQ cikin sauri suka nufi BQ niko na toge qofar falo suna xuwa nace su shigo min dashi,naga joseph yaja da baya yace oga ya gana shiga ciki fa? nace shi ne yace ka shigo dashi ciki. yana sawo kai dayan yana biye dashi da kaya niqi niqi, ya umar dake xaune kan dinning ya dube su,kai joseph wa yace ku shigo min nan? suka yi tsuru tsuru ya daka musu tsawa yace su fitar mishi a falo jiki yana rawa suka fita tare da fadin srry sir.ya juyo kaina da masifa yana cemin qatti basa shigo mishi,dan haka kaea na yarda na kuma jawo mishi wani,farida tace dan rashin sanin haqqin musulunci shi yasa ta ce su kawo mata ciki. Ni dai banxa nayi dasu na kwashi kayana na shiga daru, araina ina fadin me yasa kuka aje su a gidanku koma menene ai ku ne kuka kawo qartin,kamar kada nasa kayana cikin wardrop din, amma saidai nace bari na saka duk da cewa ni ba maxauniya bace dan ba xama ne ya kawo niba. na yaye xani dake kan katifar na wurgo shi waje nace gara na shimfida xanina, na wanke toilet din nayo wanka da alwala na fito.bayan na idar da sallah na xauna gefen katifa ina shafa mai,nayi tsaki a raina nace ko gun da mutun xai jera kayan shafa babu,bayan na gama na tuna da wayata ga yinwa na fito shi kadai ne yanxu a falon kusa da dakunansu, nace masa wayata fa? yi yayi tamkar bai jini ba,na juya xan tafi yace bari kiji ga wayar ki can kan dinning inkika yarda kika kira momy wlh tlh saina mugun saba miki,kuma ki yaqda ki ce mata wani cu xaki sani,nidai na wuce abina na dauki wayata na tsaya ina kallan abincin da sukaci shinkafa ce da miya,sai salat na wuce na nufi kitchen din.qato ne mai kyau cike yake da kayan amfani na wuta. Wata yarinya tana wanke wanke daga gani yar arna ce ita ko farida tana cikin wani dan daki dake cikin kitchen din, ina xaton store ne,dan na hango buhuhuna da kwaye, kaina tsaye na nufi gun tukwane na soma bude bude ni kaina naga qarfin halina, da yake duk neman dalili nake yi banji ko dar ba, ta juyo ta dube ni,me kika xo yimin a kitchen?ban tanka mata ba na soma neman inda xanga kayan miya,ta fita fuu nasan qara xata kai niko haka nake so in ya gaji ya maidani.store din na shiga na dauko indomie guda biyu,naxo na bude firixa na ciro kifi da nama na dafa su luguf sannan na tafasa indomi na juye ciki, duk harkan kwadayi nasan ta dama, na koma dakina naci gaba da ci ina gamawa na fito falo na je na bude fridge na ciro fresh milk na cika kofi na koma dakina.itako ashe tana xuwa tace masa gani nan naje mata kicin ita fa gaskiya ba zata yarda ba ya lallasheta da cewa ta qyale ni,ta ringa yi tamkar bata san ina yi ba, shi yasan yanda xaiyi maganina.haka nayi tayin yanda nake so cikin gidan nan. Yawanci lkcn ma basa nan ita tana xuwa mkrnt a cewarta,shi ko dama bai cika xama ba, yawan tafiye tafiye dagani sai mery yar wanke wanke da goge goge sai kukunsu, ni dai da kaina nake dafa abinda nake so dan ba komai nake ci ba,yanxu wata rana ma sai na kwaba madara da xvma shi xan yini sha, matsalata daya shine rashin kudi duk wanda momy ta bani naba su joseph sun siyo min kati na sama wayata in kira wannan in kira wancan, ya kam ina da baquwa,mina ce tace xata xo min, dan haka na shiga kicin dan yi mata mutumiyar ta shinkafar kaxa.sha biyu na gama ayukana,nan ta kirani a waya sojoji sun hana su shigowa barikin wai sai sun fadi gun da xasu je, ko su nuna kati, nace bari ma turo miki su joseph ni ina naga wani kati? da taimakon su joseph mina ta iso gidanmu,cikhn murna muka maqale juna.falo muka xube. bayan ciya ciye da shaye shaye tace taxo mana da kaset din farguni mutumiyar muce, mina ta koya mana sonta, nan muka saka muna ta rawa can tace wai ina masu gidan? nace oho,ni ina ruwana? Nace bama magana dasu, tace nifa har yanxu ina mamaki tunda jamilan ku dinnan ta qara tabbatar mana sojan nan mijikine, wai dama da auranki kika shiga skul dinmu? naja tsaki aini an cuce ni wlh duk duniya bani da wani maqiyi kamarsa, da sauri mina ta kalle ni tace sbd me? nace tun farko bana san ko ganin shi ma, sannan gashi mugu na gasu a hannun shi yanxu kam ai basu isa ba daga su har matan shi,nanfa wai xaman aure naxo.mina tace amma ai bakwa rigima ko? nake kin sanni ai tsokanarsu nake yi amma basa kula ni,itama ya hanata magana,da kika ganni nan iskanci iri iri nake musu amma sun share ni, muka saka dry.gurin 3 mina tace xata tafi gida,nace ina son qananan kaya nawa kwata kwata 2 aka sako min dayake bani na hada kayanba,kinsanni da san qananan kaya,tace dande baki da tym ne da mun shiga wani shegen boutique kinga kaya? nace dan tym inada tym matsala shine kudi, tace xo muje inada kudi a jaka,da sauri na saja wata shadda dan raramim gyale na saka shi kan kafada muka fita. Kai na rude da kayan boutique dinnan, tace gurin nan matar shugaban qasane, kaya muka yi ta jida, ina cewa ya isa, sai mina tace qara haka muka fito gun nan niqi niqi, daga nan muka wuce gidansu, sai magariba direbanta ya maido ni gida, hankalin ya umar tashe sanda na shiga gidan ya tasa su joseph yana ta masifa me yasa suka bari na fita? ya buga waya kd ance ban je ba,gashi bai san no wayata ba, saiga motar su mina ta shigo dani, nan ya isko mu cikin bala'i yana tambayar direba, shine wa? ba direba ba ni kaina na tsorata duk rashin kunyata.cikhn kidima da in'ina direba yace ni am dama ni direban amina ne, taje gidanne akace na kawota,niko da sauri na dauki ledojin kayana nayi cikin gida da gudu.farida dake xaune a falo tana cika tana batsewa, ita takaicinta daza danme xai damu kansa sad na tafi yawona? ganina da kaya yasa ta fadin sai ka shigo gata nan da tsaraba. na dubeta muka kalli juna,tace ni na sani mai hali baya fasa halinsa, daidai nan ya umar ya shigo da masifa bansan yaya suka qare da drb ba Bansan yanda suka qare da direban su mina ba, ya barshi ne ko ya saka an amshe shine? oho kun san soja da rashin imani, jin banbamin shi nayi daki kan na rufe qofa har ya shigo, wai na gaya masa daga gidan uban da nake? nace cikin gari ne gidansu mina qawata.ganin ya soma kwance belt da gudu na shige toilet, ya tsaya qofar toilet din yana cewa wa na tambaya da xan fita? nayi masa banxa ya qari fadansa yayi waje.ina jin ya fita na fito na rufe qofata ina jiya shi siida farida tana gaya masa cewa sojana nace ka daina daga hankalinka aban duk inda karya take dolene tabi maxa, kuma mai hali ai baya fasa halinshi,dama karuwa ce aka jo.... ke....ke ya katse ta da tsawa plx shut up,tsht tayi tana kallansa mamaki take yi ke dai kishin yarinyan yakeyi kamar yanda ta xata? md yasa xaiji haushi dan tace mata karuwa? alhali da shine sunan da yake kiranta,dole akwai dalili bubi yanda ya haukace dan kawai ya dawo bata nan ko ita da yaje ikirarin yana santa baya shiga damuwa kamar haka dan ya dawo bata nan. Washe gari ban fito ba saida na tabbata ya bar gidan sannan na fito haka muke wasan boya da shi har kusan wata,na kuma ma momy mitar skulsanda takirani tace zata sake mishi mgn , nace don Allah momy kice mishi inda na zabadin nan wato america nace kinga can su mina zasuje sai mu hadu binmu, tace a'a gara su 'yanmata ne ne ke ko fa, kina da miji ai abin babu tsari,ke da nake son ganin kin soma tara mana yan dagwai dagwai agidan? na turo baki naceni fa momy Allah ba xan dauwama a gidan nan ba, tace ai dama yanxun dai ki kwantar dahankalin ki zan mishi zancen krtnki ko na university nanan abj kisomazuwa,naceshikenan .yau gidan daga ni sai ni , duk da yana gari amma inazaton ya fita dan banji motsinshi ba,na fitona saka gajeran wando da 'yar shirt gurn wasanni na nufa na rnga wasana kwallon kwando na raga da tebur , na kafa daga nan na shige jim din shi donkarambani na dinga motsa jiki wani abin ma ban san yanda ake amfani da shi, amma da yake ni din ma na iya barna sai kace bera. ashe duk ya umar yana kallona a cikin wata computer dinshi dake cikin bedroom dinshi birge shi yarinyar keyi ko sha'awa take bashi? shi kanshi bai sani ba ya dai san bata bashi haushi nazo na cire na shiga wanka ya daina ganin me nakeyi domin bai lika na'urar dake kawo sakonnin cikin dakunan gidan ba sai nashikadai, naganayi gayu cikin wani siket da riga masu shegen kyau cikin kayan da muka siyo a boutique , purple ne mai shegen santsi gaban rigar a tattare take tamkar bireziya, haka siket ta baya gurin mazauna ma an tattare tsakiyar mazaunan nawa ****************************** [7:28PM, 17/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu 2----3 Na kama gashina ta gefa nayi kyau duk da ban duba madubi ba sai na hoda gareni madubin karami,nasan na hadu kicin na nufa na soma hada kayan kwadayi na, lkcn ne ya samu damar cigaba da gani na ido ya tsurawa surata domin duk motsin danayi komai na jikina rawa yakeyi , ina nasan yana gidan, kwai guda 4 na dafa na yanyanka su na zuba yaji da mai. sannanna kwaba 'yar fulawa nayi danwaken da bai wuce ishirin ba , nahada guri daya na zabga yaji na fito firij na bude na dauko dudu gora 1 , naje na ciko kofi da zuma,kan dinning naje na gabzo madara shiko dariya abin yaso ya bashi ganin yanda na tara kaya a gabana, na gama da danwaken na shiga shan dudu, na tashi da goran dudu a hannuna na kunna cd na saka discdin falguni na kure kara da karfi na shiga rawa. nan nasoma rawa kyace dama can nice nayiwakar da rawar, tagumi ya zuba yana kallon yarinyar daya tsana ada,komai nata haushi yake bashi, yanzun kam ya sani ba waiyana sonta bane amma komai nata sha'awa yake bashi. la'asar na shiga cikin dakina lkcn shima yafita gidansam bansanyana nan ba. daran ranar suna kwance shi da faridarshi kanta bisa barin jikinshi, sheka barcinta takeyi ammashi nashi baccin yayi kaura,hada hotunan yarinyar yakeyi a xuciyar shi daga sanda ta wuce su a kofar gida zuwa lkcn daya shiga yaganta ta fito wanka, waton lkcn bikin gidansu, cigaba yyi da ruwaito ta cikin mota sanda zasu abj yanda ta ringa yi komai gadara gadara ya amshe ta , haka nan sai da tazo tace ba zata zauna a BQ ba, ya tuna yanda take ta shagalinta dazun lfyr Allah. yayi juyi tare da rungume faridar shi ya samu kanshi da rayawa cewa yarinyar ce, lumshe ido yayi har saida bacci yayi awo gaba dashi . Kwanaki dayawa bai samu zama ba kuma gashi gida da ofis da gangan jikinshi suna matukar sha'awar yarinyar, danhaka ne ya saita na'urar shi yanda xata yi ta daukar mishi shiga da fice yarinyar, kurin yanaso inya dawo ya kalla kamar film, saidai cikin 'yan kwanakin nan na lura ni kadai ke kwana gidan domin tun sanda ya umar yayi tafiya faridarshi bata kwana gidan ga zatona itama tayi tafiyar ne, don haka sai naji inajin tsoro duk da cewa akwai su joseph da sauran masu gadi,nace da mary tazo mu ringa kwana tace a'a madam batasan aikin kwana akwai gidan da suna kwana nace shikenan dama tsoro na dare ne da rana kam sai barna da rawa girki kam zanyi shi kusan kala 10. in nayi wannan baimin dadi ba sai na zubar nayi wani shi kam kuku zai shigo yayi musu naso , haka nayi ta zama na har kwana 6, kwatsam ina kwance da yamma ina kallon zee aflam naga anturo kofa na zuba ma kofar ido sai naga farida ce ta dube ni ta kau da kai , nima na cigaba da kallona ,kaya ne niki niki ta shigo dasu, ta nufi dakinta ban kuma jin duriyarta ba sai can ta fito ta shiga kicin. washe gari kuma tun safe naga an hana kowa sukuni,sai gyaran gida akeyi, girki ya kasa karewa a dora wancan a sauke wannan a raina nace kila mai gidan xai dawo ne. Tun safe nayi wankina a can bayan gidan gurin da masuwankikeyi,damani bana ba da wanki da kaina nakeyi, na gama sannan na koma gurin wassanni ,nayina gaji kafin na shiga jim na dage ni a doleina motsa jiki ban ma iya ba sai dai karambani garin karfin halina naje na balla wani karfe da sauri na lallaba na fita danashiga dakina na kwanta sai karfe daya saura. nayo wanka na saka wando jeans sai 'yar karamar top fara nakama gashina da blue ribbon kalar wandon,a rainanayi tsaki nace gashii ina son naje gyaran kaina amma nasan dan bala'in nan ba yarda zaiba, ko naje nasha masifa, masifaffe,na fito na shigakicin dongirka abin da zanci , gidan ya kaure da. kamshi a rainanace yau dai 'yan gidan nan baki zasuyi ne ko? tunda nayi tunanin mai gidanne ai yashayin tafiya amma in zai dawo banga ana wannan hidimar ba, ko kuma so ne ya tashi yau? hakana cigaba da aikina ina tunani har na gama. na fito na shiga dakina,sandana shigo falon ya umar ne kandinning shi da faridar shi, ashe duk girkin dan wannan azzalumin aka yi? na tabe baki na ce dai danwani karkataccen wani na wuce daki. daren ranar daki farida ya isko ta,sanda ya shiga tana amsa waya sai dai yaga ta dan yi tsamalamar bat so ya shigo ba,ta rufe zancan dacewa to hjy sai anjima, ta kashe wayar tare da joyowa ta rungume shi yace ke da waye a waya kika shanya mijinki? tace sojana wace ni na share ka? Ya amshi wayar yana dubawa , duk dai numbers din hjiyoyine yace ke dai duk ba kya hulda da wacce ba hjy ba ce ko? ta amsa dacewa yawnci duk danginmu ne, ta saka bakinta cikin nashi ta soma janye hankalinshi da kalolin slonta, tare da gaya mishi cewa tayi missing. dinshi shi kam yana samun nutsuwa hankalinshi ya dawo jikin shi yace ta kwanta yau kam dakinta xasu kwana bari yaje yayi wanka tare da nafilfilu ya dwo, tace itama bari tayi yana fita tayo wanka tazo kan gado ta fada luu, ta fara kiran sabon kamun da tayi, cikin sa'a ya dauka don akwai shi da jin kai gashi yana sakar mata kudi kusan shine ya ture gwammnatin ahj sambo a gurinta, tace ahj jamlu dazun muna waya kaji na kama wata tashr ko? ta cigaba. wlh mai gidan ne ya shigo yace ai na gane shi yasa ban kira ba, tace ok dama na kira kane. in baka hkr yace bakomai yau dai da jiya nayi missing dinki a lot , tace kada ka damu , gobe zn fito zuwa skul zamu hadu a guest house dinka, yace nagode honey, tace nice da godiya ta kashe wayar tana tunanin irin barnar kudin da ahj jamilu yake yi kanta, ba dan tsananin son da take ma sojan ta ba, sannan shi kadai. ne namijin da duk cikin mazan da take bi bata taba samun wandaa yake skata nutsuwa lkcn hutu sai shi , ya mtukar sanin ynada ake sarrafa komai. rabuwa dashi wata babbar asra ce gareta.shiyasa bata son. ta. ga ya rabi wata mace domin duk mace da ya dandana ta kashi shi zaiyi wuya ta iya rabuwa dashi farida kenan . shi ko sojan nata Allah -Allah yake yi yayi wanka comp ya janyo so kawai yake yaga yarinyar me tayi da baya nan? domin ganinshi tamkar wani film zai kalla wanda yake tsananin saka shi cikin nishadi Sai ya kulle fofa don bayason a katse shi, tagumi ya zuba ya shiga kallon tun daga ranar da bayanan har yau, wani gurin ta bashi dariya wani gurin ta burge shi yanda take barna tana yan wake wakenta, sannan duk da bayason yaga mace tana rawa, amma yarinyr ta burge shi.sam bai san dare ya tsala ba, sai lkcn da kallon ya kare,san da ya shiga gurin farida ta jima da yin bacci, gefenta yakwanta rigingine tare da harde hnnunwanshi a kirji,fuskar shi tana kallon silin yana sha'awaryarinyar yana son ya kusenceta, yana sa ran samun rabo a gare ta, in yaso daga nan sai su rabonashi zaton. bwai yana sonta bane. Da safe haka kuwa ya fito zai fita dama ina ta gadin shi tun safe. na fito da sauri bakin kofar fita falo na same shi ya dube ni, nima shi nake kallo yanda ya sha kunu, nima haka na sha, yace lfy? nace so nake na wanke kaina don gaskiya yayi datti, ya soma tfy tare da fadin ki shirya zansa a kai ki, nayi karaf nace bani da kudi fa, ya juyo ya dan dubeni sannan yayi gaba. Da rana joseph yazo yayi ta kwankwasa kofa, na taso don farida batanan, na leka yace. oga yace kizo ga wani ya aiko don za'a kai ki saloon. ashe ma cikin barikin ne, aka gama snnan aka mai dani gida, oho ko daba cikin gari bane na dai fito dgaa wannan gidan, kullum ina cikin kamar mayya, kwanci tashi nayi watanni a gidan, inason zuwa. kd. mma yaki, haka na hakura. Yau dai da alamar farida zatayi tfy ne. ina zaune akayi ta fita da kya zuwa gurin mota, tamkar kada su rabu da mijint, sun manne juna suna ta soyayya, a raina nace jarababbu ku tafi tare mana? bayan tfyr ta shi kuma ya dawo ciki dakinshi ya shiga ya matsu da yrnyr nan jinshi yake tamkar yaje mata da bukatarshi, amma baya son raini, domin yasn da taga gadon baccinshi raini zai nemi shig tsakani dama gashi yanxun ya kul. wani. tashen balagar tsintsaye take ji, don haka take rashin kunya. wata xuciyar tace ba matarka bace? kawai kaje gurinta da dare duk yanda ta kama shi kenan amma kaje a dakenka. comp ya bude yana maimaita kallon shirmenta sanda yayi tfy, duk yafi burge shi. sai yanxun wani tunani yazo mishi wanda duk shige da ficen da yrnyr keyi bai ga farida ba, ya soma tambayar kanshi shin cikin sati dayan farida tana ina? sau 2 ya ganta, na 1 sanda ta shigo da kaya, yaga motar data sauke ta na 2 ta shiga kicin ranar kwana na 6 sai ran kwana na 7 da yaga tana shige da fice, wata zuciyar tace kasan ko tana daki ne? tunda ba shiri suke yi da yrnyr b, amma wace mota mota ce ta sauke ta? a fili yace koda yake tana zuwa skul, ya fada ne kawa sbd bayason zuciyarshi ta shiga zargi. tunda yasan matarshi ustaziya ce. kasancewar. babu mai shigo min daki shi yasa nake komai na gaba- gadi,na kan tube na shiga toilet, ko in na shiga da kaya na fito haka, domin ina da yakinin babu mai shigomin daki yanzun ma da gama wanka na dauro alwala don yin shafa'I da wutiri, haka na fito ba tare dana daura kodatowel ba, sai dan karamn dana rike a hannuna ina goge fuska Ina isa tsakiyar daki dan na isa gurin zanin sallata kan sallaya da hijabi na kurum naga mutum zaune gefen katifata, sam ban kawo cewa dan adam bane na zata aljani ne, domin kofata kulle take da karfi na soma fadin innalillahi wa inna ilaihir rajiun, Allahu la'ilah illah huwal hayyul kayyum.....nan take ya gane na zata shi aljani ne, da sauri ya tashi domin ya tsuma da ganin surar yrnyr kafaduna ya kama ya girgiza ni yana fadin ke, ke, nine fa. jin muryarshi yasa na gane ya umar ne, nan take na tuna da halin da nake ciki, da sauri na shiga neman zann da zan kare jikina hijabi na kawo na daura bai ma gama rufemin jiki bana dai daura shi haka, sannan nace lfy? shima fuska daure yace ita ce ta kawo hak! ya cigaba nazo ne na amshi hakkina, gabana ya fadi amma sai na dake, nce wani hakki ke gare ka anan dakin? yace na aure,a raina nce lallai na yarda namiji bashi da kunya, na dube shi ya manta wulakanci da cin mutunci da zagin da yayi min, na dube shi bansan inda ka ajiye hakkin naka ba, don Allah ka fita zanyi sallah, yace ni nasan gurin ya nufo ni naja bya ya kaimin wani cafka na zille na fada kan katifa yace hakan yayi daidai, yanzun zaki amince da arziki ko kin fiso da tsiya? nan tsoro ya shige ni, amma na dai daure nace gaskiya kaga banason wulakancin yanzun ne kasan dani ko baka gudun HIV din ne da kace ina da shi? kada ka manta ni fa mazinaciya ce mai zai kawo kanan? yce nima kada ki zata son ki nake ko kadan naga dai ba zan bari kina. fita bin wasu mazan ba, ya zanyi tunda an daura min ke kada kiyo yawon ki nima zunubin ya shafe n, kuma abuna gaba ina bukatar haihuwa, na dube shi nace waye zata haihu maka ni?Allah ya tsare ni. Yace nima hka sai dai dole ne ki haifa zan dauka inba farida ta musu tarbiya nace oho na gma tarbiyr ai a dakin da aka maka nan akamin, kan na rufe baki ya janyo hijabin dana rufe jikina ya yar gefe, na sakahannuwana na rufe kirjina ina karanta duk addu'ar da tazo min baki. dambe sosi muka shiga yi dashi , shi kanshi yayi mamakn karfina, ya daga ni ya mka kan katifa yce kinbi na bnza ma waje bare ni mijinki? ya soma cire kayan jikinshi zan tashi ya saka kafa ya take min kafafu, waton dama ya kyale ni ne yaga iya karfina, wayyo Allah ban ganin tsiraicin namiji babba ba is yau, duk da rshin kunyata da tsiwa ta ban taba gani ba, don haka tsoro ya kamani jikina ya soma rawa nga abin dayafi karfina, na rumtse ido na kasa katabus tunanina ya tsaya can Allah kadai nake kira, inajin shi yana juya ni son ranshi na sadakar nayi tamkar gawa ina sauraron wani al'amari dake shirin faruwa dani sai kuma me? ji nayi ya tsaya cak lkcn daya ya rungume ni gare shi kam hanyar dayake shirin bi cikin garari yaji ta bam,haka ya sakajikinshi yinsanyi tare da tunaninme kenan? ido na rufe naji tashin shi ammabansan fitar shi ba,ina. wani tunani Allah yacece nidon haka na tashi na saka kayana na kwanta kudurin zakara zai bani sa'a gobe da. safe. ya umar fa? tsorone da alajabi ya cika zuciyarshi ,tambayoyi gareshi shin wanene zai ba shi. amsa? ta 1 shin mace tana komawa budurwar ne inta kai kamar skekara 3 bata sadu da namiji ba?bayan a baya tabi wasu mazan? zuciyarshi ta amsa mishi da no, to ko yrnyr nan damabatasan wani namiji ba? y tuno yanda ya ganta da dare ranr daya bugeta da mota, ya kara tunoyanda maza ke daukarta suna ajewa kai da kmar wuya, saidai in ta komataga mene, amma bari ya kara tambayrwanilikita abokinshi kuma likitar matane. Ya tashi zumbur y dauko wayrsh layin dr bashir ya somanema ringingna2 dr y dauka tare da fdin Allah shi gfarta malamin sojoji, yyane cikin dare? yace bri kawai dr , donallah inason maka wata tmby? shinmacen datasan namiji ko maza zataiya gamewa tamkr budurwa bayanwani lkc? kamar shekra 3ko 2 ko 4? dr yace ba zai yiwu ba, ina jin kaima ka shiga rudu ne,amma ai kana da ilimi kan haka,wnnan wata hanya ce da ake kira da tantanin budurci, takanyaye da knta,sbd grmadakuma in mace mai hawa bishiya ce ko keke da makamantansu, amma duk da haka zta danji zfin yanda zata haduda da nmji tunda bata taba yiba, a takaice daiba zai yiwuba inka same ta budurwa to dama can budurwace inka same ta sabanin haka to kila ta lalacenko kuma wancan dalilin yace shi kenannagode. shiruyayicikin tunanin kenan yrnyr zarginta sukeyi shi da sauran 'yanuwanta, lallai bai taba kamata da waniba shi ya san shaidar zina tana da whl ,zato ba dole bne ya zama gaskiyann take nadama tashi gashi ya soma tuna irin wulakancnda yayi ma yarinyar,kunyace ta kama shi yanxun kafin abin nn ya faru tsakanin su sai daya gaggaya mata mgn kai zargi babu kyau, shiyasa zato zunubi ne koda ya kasnce gaskiyane. Fadar Allah da Manzonshi, ranar bai runtsa ba, haka ya kwana cike da tausayin yrnyr tare da nadamar ta a idon dangi ba zaiji kunya ba zai share mata hawaye kazalika zai cusa ma ranshi sonta, ni kam ma ai har na kwana babu barci da safe kam kinbude kofa ta nayi sai dai ana cewa maigida da gidanshi sai gashi ya bude kofar kamar ynda jiya ma ya bude ya shigo, kasa kallonshi nayi na saka kaina cikin gwiwana sbd yandana ganshi a jiya ya fadomin ya kula da haka amma sai ya share,yazo gabana ya tsugunna ya ce husna naji wani daban duk da na sani asma'ul husna ce amma babu wanda ya taba kirana da wannan sunan, ban dago ba ya zauna, kin karya? haushin shi naji tare da wani tsana, danni na tsani namijin da zai so jikina, don haka sai naji kamar na hau shi da duka,daga bisani na sakakuka yayi talallashi na a raina nace lallai ya umar wato da yake yasan yanason jikina har da lallashi na. cikin kwana kin nan sai dana ji garin abj ta ishe ni, daya fitayana Allah -Allah ya dawo wani kulawa ta musamman ya shiga min tare da hidima dani,kalamai masu sanyaya rai, duk da cewa nawa ran zafi yakeyi in yana gaya min na daina damuwa,kuma nayi hakuri kan duk abin daya min yanxun yana son muyi zama na tsakani da Allah. toshe kunnena nakeyi,nasan so yake ya samu jikina, ko ba dan haka ma ni fabana kaunar koda ganinshi ne. cikin haka faridarshi ta dawo nan ne na. kara yarda nmiji munafiki ne, ya daina shigowa ko zaizo dakina sai da dare, sannan duk bayan kwana 2 zaizo dakina nan zai kai har asubahi,na kula wato ya raba mana kwana duk randa yake dakina bana wani barci takurewa nake karshen katifa, yayi yayi dani na kwanta bazaimin komai ba amma naki [7:37PM, 17/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu 2----4 Rana laraba ya sameni xaune kan sallaya, na xabga tagumi sam ya tsani ya ganni cikin tagumi ya tsugunna, oh Allah yaxa xanyi dake asma'u? ya kike san nayi? na soma kuka,ya rasa yanda xai yi, sai ya miqe yace shikenan tashi ki shirya ki dauki kaya set hudu kixo muje,ga xatona kd xai kaini ashe dama lagos xamuje,cikin motarshi hummer jeep baqa wul,soja ne ya jamu xuwa air port cikin jirgi sai jana yake da hira har nakan yi mamakin yanda ya umar ya sauya mini farat daya, wat xuciya tace sbd jikinki ne. hotel qayatacce muka sauka, duk yanda a kayi akwai abin da ya kawo shi garin domin muna xuwa yace inyi wanka in huta in ina san cin wani abu ga wayar da xanyi amfani da ita sabis xai xo nace to. sai kusan goman dare ya shigo lkcn na yi bacci, kai ranan nayi bacci mai dadi sbd sai naji hotel din babu sanyi, ashe ya umar ne ya sakoni cikin jikinsa,saida asuba na farka,sai naji ni cikin jikin mutun qamshin daddadan turaranshi kurum nake shaqa,nayi mutsu mutsun tashi shima ya farka,hannu ya kai ya shafa gefen kumatuna Yace husna kin tashi? ya soma damuwa saboda rashin bashi amsa da nakeyi dan haka sai yaci gaba da cewa jiya na dawo baki sani ba, kinci abinci? kai na daga alamar eh, sannan na tashi, shima ya sauka shine ya ja mana sallah, da muka idar ni dashi kowa yana addu'a cikin ranshi. ni ina roqon Allah ya rabani da shi ya kawo qarshen xaman mu, shi ko roqan Allah yake ya saito mishi ni domin raya sunnar manzan Allah (S.W.A), wato aure ya dore har gaba da abada. ina kwance ina kallo yanda ya umar ke ta shiri cikin kaki, xahiri gaskiya ya umar yana da kyau, musamman in yayi shigar soja, ban taba ganin sojan da kaki ke matuqan mishi kyau kamar ya umar ba,ga tsafta da tsantseni,kullum yana nan tamkar saurayi da bai taba aure ba Ya juyo ya dubeni yayi murmushi sannan ya kira sabis dan su kawo min break,shi yace xai fita ne ana jiran shi,yace me nike so ya kawo min? nace ba komai,katin waya ya ciro na dubu biyu yace gashi na loda,kafin haka sai daya amshi wayata ya saka no shi ya kira, yayi saibin din nambata sannan ya shafi kumatuna ya tafi. yana fita nayi tsaki komai xaya yi baya burge ni, na karya nayi wanka na hau gado na soma neman layin momy dan allah kice ya maido ni, tace ba yace min kunje lagos ba? nace eh muna lagos ni dai momy bana san shine tayi dan jim, har naji nauyin gaya mata haka saidai ance magana xaran bunu, na riga na fada ta katse min tunanina nafi sanki kwantar min da hankalinki kinsan su alhj xasu bata miki rai matsawar suka ji ba xuwan dadi kika yiba. bayan haka yace kinki ki natsu ki kwantar da hankalinki,tacigaba ni kaina ai so nake in raba ku, amma ki bari sai in yayi maki wani abin na laifi, wanda xan dogara dashi. Sannan kema ki dinga yi dinga yin duk abin daya ce sbd kada yace ai baki jin maganan shi, nace to momy sai anjima. nayi shuru na so in gaya mata abinda yayi min sai naga baxan iya ba, kai tsaye na kira rahma tace amaran abuja,nace ke dai rahma da maida mutun baya kike, kin manta nice uwargida? tasa dry to yaya amaryarki da yayanmu? naja tsaki,nace kinma san me yake faruwa? tace a'a wai ki duba wulaqancin da cin mutuncin da ya umar yayi min amma na wayi gari yau wai ni yake so,jinshi kawai nake domin duk bakin da yace baya so da farko ko yace yana so daga baya qaryane,saidai dan wani abu.rahma ta katse ni, kinyi kuskure qawata, domin masana magana suna cewa,maqiyinka wata rana xai xama babban masoyinka.haka nan manzan rahama yace, in xaka qi mutun qishi dan allah, haka in xaka so mutun soshi dan Allah,kada ki manta asma-u kina qarqashin sane duk sanda ya neme ki kika bijire ma buqatarsa mala'ikun rahama ne xasu yi ta tsine miki sannan ubangiji ma tsine miki xaiyi,na katseta to ni daya dunga bani walaha? Shi kuma me xa kice? ta soma dry,baya baki haquri ba?kawai ki jure ki bada kai ke daki ka sami dami a kala, ya umar mai tsada ne wlh kin ji na rantse miki mata da yawa a waje suna san shi, domin cikin maxa dubu da qyar ake samun goma,nace ina ruwana ni kin san har ga Allah bana sonshi,sannan tunda na gane jikina yake so allah baxai samuba indai da yardata ne, rahma tace shi kenan kidai yi tunani kuma ki riqe mijinki, yauwa suraj dinki jiya naga ansa sanarwan bikinshi, tsaki nayi nace ni nama manta da wani suraj can da yawarshi, na kashe wayata. haka muka yi kwanaki hudun nan bai samu yanda yake so badai.ranar da muka dawo suka je bikon farida sbd tasan halin sojan nata xai iya shareta, dan haka ta matsa ma babansu dan ya nemi alhj dan tasam in abba ne ba xai ce komai ba, dan haka muka dawowa alhj ya tasa shi suka nufi yola.bayan sun dawo ne yace na shirya muje kd,murna na soma yiya ce amma kwana 2 xamu yi nace na yarda,gidan su muja sauka. Momy taji dadin ganina domin duk da damuwar da nake ciki fatata ta goge yanayin garin ya amshi jikina,tsarabar da yayo ban ma san da ita ba, amma fadi yake nice naya tsaraba tare muka shiga gun su mama da yamma kenan, muna nan alhj ya dawo, abin da yake bani mamaki nuna musu yake yi ina mishi tsananin biyayya sbd lkcn da mama tace tana nan tana shirman nata ko? yace ai wannan tuni ya wuce ai asma'u babu abin da xance mama sai gdy,duk yanda kuke ganin shirmanta ba haka abin yake ba, mama tace kayya ko na dai kare tane kawai faruk. washe gari yace inxo muje naga sabon gidan daya gina,wai danni daya. to wai mana, tunda dai nasan bada sunana aka gina wannan gidan ba. cikin super yellow da ratshn fari fari na saka da siket takalmi, jaka da gyale duk yellow, ya shigo yau kam ba kakin,jeans ne ya saka baqi da riga baqa yayi kyau matuka gaban rigar an rbt handsm da farin rbt,duk da ba sanshi nake ba ya burgeni kuma nasan shi din handsm ne, raidai bana sanshi. Yana murmushi ya dube ni zo muje husna, fuskata bbu walwala muka. fito yace momy sai mun dawo tace to sai kun dawo ni kam banyi ko mhn ba, domin nakula momy tasauka ganin yanda yake matukar nuna kulawar shi a kaina, a raina nace bata san cewa abin ba dan Allah bane son kawai yake yi ya same ni daga nan yayi watsi dani kokuma in haihun kamar yanda. yace, ya bama farida din ni kum ko oho. anty amarya ma tace sai kun dawo dan gidana, yace to antyna. ya riga ni fita saboda yanda nake tfy tamkai kwai, sallamar wasu dattawa tare da matasn layin wanda dama ya saba da musu ihsani duk sanda yazo hakan yana ban sha'awa domin na sani ya umar akwai kyauta, taimako dakuma sadaka, kusan yaran gidan mu da nasu, duk shi ne ke dauke da nauyin karatu da suturunsu, haka nan abincingidajan 2,duk wata yake lodemusu komai. ya umar yana dahanyoyin kasuwanci da hannun jari donhaka kudi ko taina suna shigo mishine,ko 'yan bauchi zuwa gombe dangin uwa da uba yana taimaka musu, 'dai'dai ne wanda ya umar bai kai makka ba a danginsu, shida farida kuwa ummara da hajj bansan adadin zuwansu ba,tunda ni lkcn ina Tunda ni lkcn ina skul lkcn ba zance ga yawan zuwansu ba, duk a lkcn ne yakara kai su mama dsu momy wannan shine dalilin dayasa ya umar ya zama tauraro ckin dangi har da mutanen unguwa, yammata na unguwarmu duk sunamin sam brk da samun miji kamarshi, ganin su nayi dace kuma nazo duniya. da hannun dama. ni kuma gareni bani da burin da yawuce yace asma'u na sake ki saki 3. na tsaya jikin motar , ya juyo ya dubeni ya sakarmin murmushi, tare da fadn , asmy kn fito?na dauke kaina gefe ya iso da sauri ya budemin gabanmotar na shiga ya gyaran gyalena da ya sauko kasa sannanya rufemin ya koma gurin mutanen yana fadin 2mins .kallonshi nakeyi yana rabon kudi tare da sauraron matsalolin wasu, ya gama ya nufo motar, su na ta godiya dasa albarka, wani tsoho yana fdin, Allah ya azurtaka da 'ya'ya masu albarka, ya sake juya waya dubi tsohon sannn yace amin ya Allah. ya shigo motarya zauna ya dubenida murmushi yarinya kina ta jira ko? sorry bari muje ko? banko dube shi ba na tabe baki shima yasan bazan tanka ba don haka yajamotar muka dauki hanya, duk inda muka wuce matasa da ymmata kallon motar sukeyi nasan tana da kyau ,amma yanmatan wsu sunakallon maimotar ne kila birgesu su yakeyi ,ni kam kinshi nakeyi . A zatona new extension gidan yake ashe tfy ce mai nisa har gwamna rd , gidan tun daga waje ya soma birgeni yyi horn mai gadin ya bude soja ne muka shiga , kallon gidan nake daga gani kaga tsarin turawa,ya fita. ya zagayo ya bude min, kan na yunkura ya dauki jakata na fito yana rike da jakata muka shiga gidan, ban taba ganingidan daya tsaru kamar wannan ba tunda nake shi kanshi yasan gidan yamin, yanda yaga shagalada kallon gidan . mun shiga bangare bangare na gidan gurin wasannin yara ma gari guda ne ga jim ga gurin wasanni abin sai wanda ya gani, an gama komai har ankawo kayan kicin duk suna cikin kwali, ina tsaye ina kallon yandakicin din zai tsaru in an jera mishi wadannan kaya, sai naji an rungume ni ta baya na rasa duk sanda ya tabani sai ntamkar kaya ya sokamin, nan da nanna hada rai yace kinga gidan ko? na daga kai alamar eh yace jim dinnan daga baya nasa akayi sbd naga kinason motsajiki, na dago kai na dube shi a raina nace yaya akayi ya sani? tamkar yasan tunanin da nakeyi sai yace yaya bazan san niba bayan ina sonki? kece baki san inasonki badon haka wannan gida nakine keda yaranki , na dubeshi da sauri na kara bata rai y sake ni ya dawo gabana bakison yara? Na soma tfy yana tsaye a gurn yana kallona banwaiga ba na sauka kasa,na fito naje na jingina da mota,shikam tsayawa yayi yana kallona ,har na kule ranshi ya sosu, ammaa shi kanshi yanxun yasan son yarinyar yakeyi gashi duk sanda ya roki haihuwa wurin ubangiji ita yake gani a mafarkin shi tana miko mishi kyawawun yara , don haka lallashin ta xae ringayi kamaryanda antynshi ta bashi shawara, sannan xai hada da yan dabarun su na maza,yayi murmushi daya tuna yanda xayi ya shawo kanta ina kallonshi har yaiso gurina rike da jakata ,bude baya yayiya shiga yace shigonan asmy, na dubeshi fuskata babu walwala yace meyasa bakison haihuwa dani? ki gayamin gaskiya . [7:38PM, 17/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu 2----5 Ba tare da natuna mgn ba nace ni banason ka ne, dim yayi na tsawon lkc na sani sam baiji dadin kalmata ba, a raina murna nakeyi Allah yasa yayi zuciya ya sakeni, yace meyas bakya sona? nayi shiru yace sbd laifukan danayi miki? na sunkuyar da kaina mgn kasa kasa na keyi nace ko bama haka ba dama ni tuni can bana sonka,ya saka hannu cikin aljihu ya ciro hankici ya shre zufar data tsattsafo mishi gurin goshi.toh shi kenan xanyi tunani yanzun inna sake kina da wanda kikeso? na dube shi fuskata a dan sake nace a'a zan koma skul ne yace shi kenan zansan me xanyi akai ya tashi yace koma gaba mu tafi, duk muka koma gaba ya tashi motar bayan ya saka disc din karatu cikin suratul najmi, muryar wata yrny mai tsananin zakin murya, mai gadi yana mishi mgn sam bai kula ba don nasani yana cikin damuwa, ni kam raina kar nasan dole yayi xuciya ya sake ni. Tun dawowarmu ban ganshi ba da na zata yau zamu koma sai naji shiru...shi kam tunda ya idar da sallar isha'i yana kwance kan doguwar kujera dake shashen baqi yayi zurfi cikin tunani.tabbas yarinyar bata sonshi tunda ta iya buda baki a gabanshi tace bata sonshi me ya kamata yayi yanzun?ya tambayi kanshi,zuciyarshi ta amsa mishi da cewa kurum ka sake ta dan baza ta taba sonka ba wata zuciyar ta tambayeshi cewa yaya zaka yi da sonta?ka sani dai yanzun kana matsanancin sonta sannan ga dukkan alamu itace uwar 'ya'yanka shikenan ka hakura da haihuwar? take nan daya sashen na zuciyarshi ya amsa mishi da cewa sai ka auri wata,ya furta da bakin shi hakane zan iya auran wata kuma ta haihu Ya tashi zaune dama cikin duhu yake ya kashe wutar falon,ya dauki wayarshi dake gefan shi ya kunna neman nambanta yakeyi karo na farko a rayuwarshi,lokacin kwance nake cikin kayan bacci riga da wando masu santsi na dora rigar sanyi a samansu.na kwanta ne kan gadon momy ita tana zaune kan sallaya hannunta riqe da carbi,wayata ta soma ruri na duba babu suna, na dauka tare da fadin hello saboda bacci da ya dan soma dauka ta,dim ya yi domin muryata ta ratsa tun daga kunnenshi har yan yatsunshi. Yace asmy inason ganinki yanzun,jin muryar yaya umar na wartsake bai taba kiran nambata ba,don haka na yanke hukuncin saki ne zai bani, nace kana ina ne?yace shashen baki nace to gani nan,momy na kalla wadda tun shigowar wayar ta zuba min ido nace ya umar yana kirana tace to cikin fara'a ga zaton ta na soma saukowa ne na fito na saka silifas dina nayi wajen baki na bude kofar falon duhu dindim falon nayi sallama ya kunna wayarshi tare da amsawa,yana kwance bai tashi ba na isa gurin da Yake nace gani ya tashi zaune ya matsa yace zauna na zauna ba tare da wani dogon tunani ba, ya zubamin ido yana kallona na gane yana kallona ne ta hanyar yanda ya haske min fuska da waya kusa minti 6 bai ce min kala ba, har na soma gundura da zaman na dube. shi zanyi mgn muka hada ido na sunkuyar da kaina sbd idonshi yana da wani kwarjinina musmman fasa mgn nayi ya ambaci sunana asmu, na dube shi yace zan miki abin da kikeso. na zuba ma fuskrshi ido sannan farinciki ya bayyanakan fuskata. na kula har mamaki abin ya bashi ya soma shigo da dabarunshi yayi tunanin amfan dasu yace amma kfin in baki saki kin tanadi abin da zaki gaya ma su alhj da abba da momy da kuma mama? gabana yayi muguwr faduwa sbd sam na manta da wannan matsalar, idona ya rufe ni dai burina ya sake ni, yayi murmushn mai sauti yace me za kice musu? in kin tanadi amsar da zaki basu to yanxun in baki sakinki. jin haka yasa nace ka bani kwai ni nasan me zance musu, na fada ina duban fuskarshi yace a'a sai naji tukunna,na sunkuyar da kai inawasa da yatsun hannuwana nace zance kwai ka sake ni ya jeho min tambaya da sauri kan wani dalili? Na dube shi nace ban ganeba, yace insuka ce kan wani dalili na sake kime zakice? nce zan ce ba komai yace kin taba ganin anyi saki babu fada? nace a'a zance nice na ce ka sake ni, yace to in sunce meyasa kika ce na sake ki me zaki ce? na ce zance sbd banason ka, yayi shiru sbd kalmar tana mishi zafi, yce toh shi kenan zanbaki yanzun, amma kin tanadi gurin zuwa? na dube shi cikin rashin fahimta, ya cigab kinmanta batun alhj da suka ce inkin kashe auranki ki nemi gidn uba? mama cewa tayi ko danginta kada kije bare alhj daya ce ya cireki daga cikin 'ya'yanshi. numfashina sai da ya nemi ya dauke sbd faduwar gaba na saka hannu na rike baki sam na ma manta yayi 'yar dariyar nasara, ni ko dan shirme sai nace to baga nan gidan ba? na cigaba ai dam na dade wurin momy ka manta? nan yamin kllon yarinta, yanzun ne ya gane wannn karamar yarinya ce, kuma cikin lkc kalilan zai mata wayo, ya jehomn min tambaya shekarunki nawa? na dube shi sannan nace 18 da wata 7 a zatona harda shekaru ake rubutawa cikin takardar sakin shi kam ashe wauta ta ce. ta saka shi tambayarta jin haka yayi murmushi laillai yarinta ya raya a ranshi, ya sake Ya sake cewa hakane na tuna anan gidan kike zama, sai dai kuma kina ganin za ki iya cigaba da zama da momy bayan kince baki son danta ina nufin ba zakiji kunya ba? nan take na gano kuskure na in har nasan kunya lallai ne nabar gidan nan to ina zani? zuciyata ta amsa min sai ki shiga duniya. na daga nace ba komai ka bani kawai zan tafi koma ina ne. da sauri ya dube ni, kina nufin zaki shiga duniya? nace eh, yace can cikin duniyar zaki samu ci da sha da gurin kwana da kayan ado da kuma uwa uba karatun da kike so? bari kiji in sana'a zaki kama shekara nawa zaki yi kafin ki samu registration, balle je batun skul fees, banda books, nan mana gano kurena, nayi shiru kawai yace inbaki ne? na dube shi to kai baza ka taimaka min ba? yayi driya sannan yace haba asmy cewa fa kikayi baki sona sannan kuma kice in taimaka miki? nace ai naga lkcn da baka sonama ka taimaka min na gama secondary, yace to wannan baki ganin lkcn kina da aurena a kanki? yanxun fa rabuwa zamuyi kin manta? na sake yin shiru yace to yanzun ya ya za'ayi? na dai kasa mgn dan naga gano bani da mafita, duk mun yi shiru gidn ma yayi tsit domn dama dre yayi Can yace ga mafita da sauri na dube shi in gaya miki zaki yarda,kuma zki yanda nace? na gyara zama me zai hna in dai zaka sakeni? yce zan sake ki mana, nace to ina jin ka yace zan biya miki kudin skul har ki gama zan dauki nauyin yi miki komaihar ki gama duk karatun da kike so, sannan kuma zan cika miki burinki na sake ki, in har kin yarda ki zauna dani ki haihu, kina haihuwa zan sake ki, kuma in cigaba dabiya miki kudin makaranta sannan zan gaya ma su abba cewa nine na sake ki don kainaba wai don kin min komi ba, na ce to in ban haihu bafa? yace nan da 2yrs sai na sake ki to karatunfa? yace daga mun koma abj zan nema miki jami'a ki fara inmun rabu sai ki tafi inama kika ce ? nace america inda su mina suka tafi yace ok, to me kika ce? nace to zanyi tunani za gobe, yce shike nan. tashi kije ki kwanta. sanda na shiga dakin momy tayi bacci ko kuma tana jina tayi shiru ne? oho na hau gado na kwanta shiru ina son yin tunani ne game da magarnar mu da ya umar , damuwata daya yanda zn jure zama dashi har na haihu, ko kuma in ban haihu ba yace 2yrs sai ya sake ni kuma yace zamn 2yrs xan mishi biyayya zan iya kuwa? Na sake juyawa naci gaba da tunanin in ba a wannan hanyar ba saidai in shiga duniya ga tsinuwar iyaye, hka nayi ta tunani har kusan asubahi, amma ban tuno wata hanya mai sauki ba, bayan na tashi saidai na yanke zan kara tuntubarshi da safe koda text ne inji ko zi taimaka min a zaman da zamuyi kada ya kusance ni? da wannan tunanin nayi bacci. shi ko ina fita yayi dariya sannn yace yaro dai yaro ne,ban da haka yaushe zata yarda da wannan mgn mai kama da tatsuniya, fes ya kwanta zuciyarshi tana shaida mishi ta same ta matsalar shi daya ce son da bata mishi, saidai yayi alkawarin shi umar faruk zai koya mata yanda zata so shi. da safe ina karyawa momy tace in ba da wuri zaku tafiba ki kwanta ki huta mana?na dube ta ban san sanda zamu tafin ba, amma na gaji jiya banyi barcin kirki ba, momy dama tasani shi yasa take son jin shin me ya hana ta barci, don duk tana jin motsnta da yawan jan tsakin da takeyi sai tace me ya hana ki bacci jiya? a shirme na da zan gaya matane sai wayata ta soma ruri na dauka muryan ya umar ta sauka cikin dodon kunnena, karki sanar da kowa halin da muke ciki,inason ya zama sirri nace to ni ma zaka ga text dina yace ina jira. Na dubi momy dake jiran bayani nace me ma kikace momy? tace cewa nayime yahanaki bacci jiya ko baki jin dadine? nace kaina ne ya danmin ciwo, sai na share mgnr, shi kam ya umar jikinshi ne yabashi xaniya fadama momy, shiyasa ya katseni kona ce yayi min kashedi. na fito wanka ina zaune bakin gadoina shafa mai nan na tuna da text din da zanma ya umar, na rubuta mishi cewa donAllh ya umar ina son kayimn wani taimako daya? in har zakamni toh xan amince da shawarar jiya , na tura mishi nan da nanko sai ga amsa ya turomin, sai na tura mishi cewa in har ka yarda zaka kyale ni ina nufin ba zaka kusance ni ba, na tura mishi sai gashi ya kirani kamar kada na dauka sbd nauyin mgnr takemin, amma sai na dure na dauka yace asmy kina jina?nace eh,yace ai wannan ba zai yiwu ba, taimkon da zaniya yimiki kenan, ki haihu min ni kuma inbiya miki skul in wanke ki gurn iyayenmu bayan na sake ki, kin yard ko a'a? yaci gaba da fadin ina lallaba ki ne kawai amma kin san matata kike addini ya bani dama ko da karfine in nuna gurin saduwa dake wato in kika ki kenan,na dai duba laifukan dana miki ne na baya shiyasa nakeson wanke kaina gurin ki, [7:40PM, 17/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu 2----6 Amma in kina son haka zan miki ya dan kausasa muryarshi,sannan yace ki zaba ko yanda nace ko kuma mu mukoma inta nuna karfina ina saduwa dake kuma ki samu cikin ki haihumin, sannanbaxan sake ki ba babu kuma karatun inma naga dama duk shekara sai kin haihu da yardar allah. .da sauri na ce don allah kayi hakuri na yarda a na farkon yace shi kenan,na zabga tagumi ina tunanin ta ina za'a fara?bayan na shrya,ya umar ya shigo yana sanye da kaki yace zai je ya dawo na zama cikin shiri ni kunyarshi ma nake ji tunda wannan zancen ya shiga tsakaninmu yana tafiya momy ta ciro wani galan cike da wani abu da naji tana kira tsumi tun farkon aurena da ya umar take dirka minshi sai dai in banzo garin kaduna ba ko hutun makaranta nazo lokacin sai ta bani nasha,niko uwar kwadayn zuma tabani na cewa yauwa momyna kamar kinsan nayi kewar wannan tsumin na ce yauwa momy na kai kamar knsan nayi kewar wannan tsumn na diddilo a kofi na soma sha A mota yana ta jana da fira na dake nan take yayi min tuni cewa har da fa biyayya cikin sharadin shi kuma dole ne in ya min magana na ba shi amsa,kuma na saki fuska,nace to a raina nace zanko iya?...Mun iske farida da kawayenta su lady na rigashi shiga ciki saboda ya tsaya gurin su joseph,su farida surutu yaci karfinsu dan haka basu ji shigowata ba.lady tana cewa ai ke naga sakarcinki yaushe zan samu miji kamar naki sannan in tona kaina,ki dubi yadda ya yarda dake,yana alfahari matarshi ustaziya,sannankina sha'aninki da abokan harka yadda ranki ke so,kudi suna shigo miki yadda ya kamata,sannan ki tsokani fada?dayar tace kyaleta lady,farida sakaryace kina zaton da zaki kashe auranki su haji jamilun auranki zasuyi?lady ta amshe da cewa yaushe zasu aureki duk kyanki sun fi son su auri kananan yara suna tsotse su,ba gamu ba sun yarda harka ta duniya ayi ta amma da kin yi musu zancen aure yanzun nan sai ku bata,Farida tace nima tunanin danayi kenan shi yasa na matsa na dawo., Domin alhaji sambo ya ce ynxn sunfi yayin hulda da matan aure,Lady tace sosai ma,baki ganin yanxun knfimu abokan harka farida ta ce hakane,dayar tace ina xaton kila wani sihirine 'yan iska ni zan gaya muku haka,domin watarana ni da wani wawa kum ma sanshi dan iskan ministan nan tsohon banza,lady ta ce ATY kike nufi ko?ta ce eh shi mana,har fa mun soma harka sai dan iskan kawalinshi ya yi mishi waya wai ga matar aure nan ya dagani ya bani dubu goma,na ce Allah bai isa ba bazan amshi ten ba shine ya ce to in jirashi..Ke a takaice gabana ya ba matar auran nan dubu dari da hamsin dana soma tsiya sai yace koni da ina da aure haka zai bani da na so insan dalili sai yace wannan wani sirri ne don haka kada na daga hankalinki kan wannan yarinyar,lady tace ki dae hada da kisisinar da muka gaya miki suka yi dariya suka tafa,ni dai kaina ne ya daure,shin harkar me farida ke yi?irin wacce kawayenta ke labari yanzun?sallamarya umar tare da rufe kofar da yayi da karfi ce tasa suka waigo,ya dubeni asmy yaya baki shiga ciki ba?ni dai kallon su farida nike yi lady ta zungureta da hannu nan da nan ta tashi ta nufi ya umar da sauri tana fadin sojana kun sha hanya ta dube ni shigo mana asma'u Ta amshi jakar hannunshi ya dube ni kije dakinki tafiya nike ina kallonsu,ya shafi gefen kumatunta tare da fadin i miss you,ya dubi sashen su lady ya ce yau su malama hafsa ne a gidan na mu? tace wlh munji shirmen da faridar taka taso tayine shi ne mu kazo don mata nasiha banda abin farida duka duniyar na wa take?ya ce a ton kuda ku ke waje ku za ku fita sanin me duniyar ke ciki,dayar ta ce tabbas mun gaya mata,su ka kalli juna su da farida naga sun kashe ido,tace nima ai nagane kurena kuma na bada hakuri ko sojana?dama shi ya dauki hanyar zuwa dakinshi daga can ne yake fadin hakane my farida,dama rigima ai ba halinki bane,ya shiga daki ta yi musu alamar tana zuwa da hannunta itama ta shige suka juyo dubansu gareni inda nike tsaye rike da kit dina..Suka kalleni suka tabe baki,na tura kofa na shige,Lady ta dubi dayar tace kinsan allah Sara inda nice farida tuni zanyi waje da shegiya,ba boka ba malam tsabar kissa bare ga shaidar dakamin ita kuma ga mummunan tambarin daka kamata ai sharri kala-kala zan dinga hada mata,Sara ta ce ke bari irin yarannan sune ake ce ma dan hakin daka raina sai kiga yarinyar ta kere ta,amma tana da hanyar da zata ma yarinyar korar kare.... Farida ta dubi sojanta don allah ka ba Asma'u hakuri dan yanzun kunyar yarinyar nake ji bai dace ina babba in dinga zubar da mutuncina ba,ya dube ta cikin farin ciki ka da ki damu,dama yana da kyau mutum in ya yi abun da bai dace ba,in an fahimtar dashi ya fahimta sannan ya nuna yayi kuskure,ta ce hakane nima banyi amfani da hadisin nan ba, Farida ta dubi sojanta dan Allah kaba asma'u haquri dan yanxu kunyar yarinyar nake ji bai dace ina babba in dinga xubar da mutuncina ba,ya dubeta cikin farin ciki kada ki damu, dama yana da kyau mutum in yayi abu da bai dace ba, in an fahimtar dashi ya fahimta sannan ya nuna yayi kuskure, tace haka ne nima ban yi amfani da hadisi nan ba, wanda ya hore mu da soma dan uwanmu abin da muke soma kanmu, kishi ya hanani ganin gsky amma insha Allah daga yau na daina xan yi koyi da irin kishin da matan manzon Allah sukayi.da sauri ya juyo ya rungume ta tare da fadin shi yasa kullum nake qara sanki my farida, kuma ina san ko ba kece kika haifa min yara ba xan baki su ki musu tarbiya ta qwarai, tace na gode. bari inje muyi sallama dasu hafsat gida xasu je, ya jawo dirowa ya ciro kudi ya miqa mata gashi ka basu, haka ake san abota da mutanan qwarai,gasu cikin shiga ta mutunch, ta isa gunsu tana dry suma suka soma dryr tace shegiya ni ,sukace me ya faru yar iska mai fuska 2 Ta koro musu komai suna ta dry,sara tace har yana cewa munyi shiga ta mutunci bai san saida na koyi yanda xan saka hijabin nan ba? lady tace ni xafi ma ne duk ya dame ni muna fita daga barikin nan xan cire shi,ta miqa muru kudin ga shi kinsha sigari, sara tace gara mu ke fa shegiya me juye giya a kwalbar cocacola tace naji ku tashi ku fitar min a gida,ta raka su suna mata tsiya itama tana musu.ina cikin juyayin me xaije yaxo ne a cikin wannan xaman da xanyi danake mishi laqabi da xaman waqafi. bayan sallar isha'i, xaune nake na hada tagumi wayata ta soma rngng, na duba na hadda ce no ya umar amma ban haddace tawa ba, na dauka yace asmy ki fito ga munan a dining nace na qoshi fa, yace ki fito kawai kinsan kina cikin sharadi ne, na fito jiki ba qwari na ajiye hijabina,riga ce da wando na kamfala rigan kamar ta maxa aka dinkata iya cinya wandan kuma fela na kama gashina da dan kwalin sbd ni ban cika san daura dankwali ba Zamanta kenan nima na iso gun ya nuna min kujera xauna na xauna kusa da farida,ta xuba mishi tuwon shinkafa miyar ogun, ga nama manya ta xuba mashi farfesun kaji, ita kuma farar taliya ta xuba da miyar kayan kayan lambu,sannan ta saka soyayyan naman kaji ta dubeni da fara'a me xan xuba miki qanwata? nace a qoshe fa nake ni,tace me kika ce? shuru na mata shi ko sai ya cika kofi da fresh milk ya miqo min da strw na xuqa, yace kinga irin nata nan, kinsan ita ba komai take ci ba,dama dai dan wake ne a yanka mishi qwai.da sauri na dube shi a raina nace waya gaya mishi? ban gama mamaki ba naji yace kinsan ko farida yarinyan nan ba girkin kowa take ciba,domin ko ita ta hada abinta in bai mata ba xubarwa take yi ta dora wani,na saki baki ina san tuno wanda ya gaya mashi, to waye domin ba kowa sannan shi bayanan. na kalle shi yayi min murmushi yaci gaba da cin abincinshi, yanxu kuma ya s6a bani tsoro domin ina xaton qila yana da aljanu,domin haka ranan da mukaje ganin rabon gidan nan yace jim da gun wasanni sbd ni. Dan yaga akwai ni da san xuwa jim,nasan ko su joseph basu san ina xuwa gun nan ba, inko sun sani waya gaya masa na girki...ya ketse ni,tunanin me kikeyi kisha mana, in kuma kinfi san ki xuba xuma da madasa to kije ki dibo na tsura mishi ido, ya dake tamkas ba shi yayi maganar ba. jiki babu qarfi na dauki strw na soma shan madara, araina nace allah abin tsoro ya umar abin tsoro, sai kace mai gani har hanji, ina jinsu na soma hamma, yace bacci ko asmy? na daga kai yace tashi kije ki kwanta, farida tace ya dace a sa mata ko da gado ne kadai a dakin,yacf nima nayi wannan naxarin,ni dai kallan su nakeyi, araina nace ke kika sani da munafincinki, na kwanta na toma bacci naji turo qofar shi yaxo ya tsugunna gabana ya shafi gefen kumatuna sannan yace asmy saida safe, ya fita yaja min qofa,washe gari da kamar sha biyu shi baza na dan tun safe yayi tafiya sai gnbe yai dawo, haka ya gaya min lkcn dana fito wanka da safen sanda yaxo yimin sallama,wasu mutane suka shigo su biyu sun sami farida tana shirin fita. Joseph ne yace yawwa madam ga baqi nan xasu miki bayani, ruka sanar da ita cewa oga yace suxo su duba dakin amarya, ta nuna musu sannan tace suje,sun shigo suka min sannu sannan sukayi ta yan gwaje gwaje suka tafi, washe gari sai ga su sun dawo da kaya niqi niqi fita nayi na basu gu suka yo waje da kayan dakin suka shiga shirya dakin. kusan 3hrs sannan suka tafi.da sauri na shiga dakin domin daga yanda nake ina kallansu sunata aikin shirya dakin, tsayawa nayi galala ina kallan yanda aka kafa gadan. mamakin da nake ban ga sun shigo da kayan gado ba, da kwalaye na gansu amma sai gashi sun tashi gado da wordrop,mirror ga labulaye masu shegen kyau suka dora min katifata suka shimfida gado,gsky dakin yayi min kyau, na fito na kwashe kayana na xubasu cikin sabuwar wordrop. misalin qarfe hudu da rabi na idar da sallan la'asar ina xaune kan sallayar qara kallan dakin nake yi, araina kuma ina naxarin kudin kayan nan ko xai kai nawa?wayata ta soma ringing watona momy ce sai naga no din ya umar ce, Gabana ya fadi domin kwana dayan nan da baya nan ji nake tamkar an cire min qaya na dauki wayan nasa a kunnena bance qala ba shine yace hello, nace ina jinka, yace ina hanya a kiyasina nanda xuwa 7 xan iso da fatan baki manta cewa yau kece da miji ba?gabana yayi mugun faduwa,nace ni ce da miji fa kace? yace yes kwana 2 2 xaku dunga yi keda my farida, kada ki manta cikin sharadi kike tare da bin doka duk abinda nace maki to yaune doka xata fara aiki ,kuma dama na gaya maki ko shekara daya kikayi kina bin doka rana daya kika karya to fa wannan shekaran ta xube sai kin kuma wata shekara biyun, ke ko gobe shekara biyun xata cika kika saba sai kin sake wata 2. tamkar xan fashe da kuka domin har hawaye ya wanke min fuka,nace kai ya umar wlh ba kace haka ba fa,Allah ko ranar da muka yi maganar a kd bakace haka ba fa, tamkar xai kwashe da dry yace to na manta ne yanxun gashi nan na fada miki.dan haka sai ki shirya mun tebur in kuku ya gama in kuma nima xa amin madara da xuma dinne to sai na iso ko? See Translation [7:41PM, 17/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu 2----7 Shiru nayi shi kuma ya katse wayar,kuka na saka na farko ga rashn son da nake ma ya umar ga kuma fargaban yadda zamu kwana gado daya,na mike ina 'yan gungunai shi ya umar dinnan ya cika wayo,bayan ba haka muka yi da shi ba zai ce wani in na karya doka sai na sake daga farko,haka nan jiki babu karfi na kira Rahma,ta san komai yadda muke ciki da ya umar cikin kuka nake gaya mata dariya ta shiga yi min domin ganinta hakan da ya umar ya yi shne dai dai,nace haka ma zaki ce?Tace to ni bnga abn ki agun ya umar ba,na ce Rahma ni nasan irn wuya tare da bakaken maganganun da na sha gurin ya umar,ta ce wannan kina lbrn abnda ya wuce ne,na ce gunki ko?don ni gare ni bai wuce ba,knsan Allah? bana son ya umar bana kaunarshi,wlh don dole nake ganinshi,ta ce lallai kina da aiki Asma'u.A haka ne zaki cinye shekara biyu kina biyayya?na ce shne nake tunani gashi ya ce ko na fi shekara indai na saba na rana daya to na rusa wancan shekarar na baya,ta kwashe da driya ta ce ai dama hakane dokar,Allah ya ba da sa'ar cin jarabawa,na kula harda iskanci take min dan haka sai na kashe wayar,na idar da sallar isha'i na shiga kicin kuku ya gama komai na soma jidowa ina kawowa dining...Ya Umar ya yi sallama fuskarshi cike da fara'a,na amsa zan tafi kicin ya ce asmy ba ki ganni bane?na ce sannu da zuwa,bai amsa ba ya iso guri na ya ce haka ki kaga my farida tana min?tana amsar abn da ke hannuna bayan ta rungumeni yayi kasa da murya tana kaini daki ta min wanka.da sauri na kalleshi sannan na sunkuyar da kaina ya ce kada fa ki manta kina bin doka ne. Na dube shi nace zan dai karbi jakar kawo amma gaskiya ni fa ba zan iya yi maka wanka ba. yace to rungume ni fa? kin dai san b zan miki afuwr abu 2 ba,na rasa yanda zanyi domin niba ma bazan iya rungume shi bane, zan iya amma rashin son da nake mishi ne yasa ba zan iya rungume shi ba,sai naji ya manna ni da jiknshi, yay kiss a kumatu na amshi jakar shi, sannan nayi hanyr dakinshi, yace rana ta farko dana shiga dakinshi. dakin ya tsari fiye da yadda zuciyata take rayamin a da, ina kokarin fitowa ne suka shigo shi da farida tana rungume dashi,na fita naa basu guri ko kusa banji haushi ba, domin sai kana son mutum ne sannan zakali kishinsa. sai da nayi sallar isha'I sannan na fito,na dai yi wanka ammabanyi wata kwalliya ba domn banason yayi sha'awata , doguwar riga na saka jallabiya baka na daura dankwalin rigar a kaina na fito,tuni sun so kan dinning din. ina zuwa kafinna zauna nasoma zuba mishi abinci kamar yanda naga farida ta mishi jiya, Yace good sauran ki zuba ma my faridada dan yatsina baki,no ki bar shi kawai zansa da kaina, ni kam fargaba ya hana ni cin komai duk da sha'awar kus-kus din ya bani fresh milk din dake kan dinnin dinshi na janyo na zuba cikin kofi na soma sha. ya umar ya kallo farida yace yrnyr nan 'yar madara ce, ta taba baki batace komai ba, na kula taji haushin yanda ya umar ke min ni kam data san haushin da shi kanshi yake bani da bata damu kanta ba. an gama cin abinci na tashi na shige dakina jim kadan ya shigo kai tsaye ya zauna bakin gado ya dubeni, kinyi shafa'I da wuturi? nace eh yace kije kiyo alwala muyi sallar ma'aurata, da sauri na dube shi yace ko ba ki shirya shiga skul ba? nace na shirya mana yauwa sai ki dinga cewa to kawai duk abin da na saka ki matsawar bai saba ma addinin musulunci ba, shiru nayi sannan naje nayo alwala munyi sallah ya jma yana addu'oi sannan ya dube ni, Allah yasa yau ma ki samu cikin kinga kin huta kenan ko? idanuna sukayi rau-rau nace to muryata ma rawa take yi duk da boye dariyar da yake yi saida ya dan dara, a raina nace mugu ba dole ka min dariya ba, ya zauna bakin gado yana kara kallon dakin ya dube ni gaskya marhaba sun iya tsara guri, Dakin yayi kyau sosai ko? nace um, sbd jin shi kawai nake ni duk cikin fargaba nake. ya dan sha mur sannan yace bki fa zaki rinka budewa kina min mgn nace to, amma cikin raina fadi nake Allah ya shiga tsakanina da kai mugu, yace taso na tashi yace zo nan, naje jikina sai kyarma yake, yace wannan rawar jikin fa kamar kinga dodo? na dai yi shiru yace cire kayanki, a tsorace nakalle shi na soma kuka yayi kini -kini da rai menene na kuka abin nanba dole zabi na baki kika yarda in kinga ba za ki iya ba to na baki saki ki kije ki kare kanki gurin su alhj sannan kudina ya huta na jami'a dinki. gashi dakyar ma na samu form din, jin har an samo min form yasa na soma cire su, nasoma yarfa hannu irin yanda mutum ko ince yara ke yin suna jin tsoro ina kuka ya taso ya rungume ni ke kin cika tsoro , ba wata wahala zan baki ba in dai kin saki jikinki kai na matukar tsorata hakan yasa shi kwatar dani a jikinshi yana lallashi na har na dan nutsu ganin bai komai ba sai 'yan wasanni da yayi ta min haka muka kwana washe gari ya nuna min formdina har ya cika yace in dai ina bin yanda yace nan da satin da zami shiga zan soma zuwa skul, nace to nan ma ya rungume ni Tare da min 'yan wasanni shi dai ke kidan shi yake rawarshi. yau ma kamar jiya cewa yayi kadamana saka koma bayan da zanyi dolenayi yarda yace wasanni yakedani son ranshi danaji zai wuce gona da iri sai in saka kuka daya koma gurin farida,ranar ni na samu ishasshen bacci sbd fargaba daya na gunana kasa bacci,ke cikn kwana 2 har ramanayi banacin abinci ko yaushe cikin tagumi da tunani wannan karon daya kara dawowa guna cewa yayi duk abin daya min nimasai na mishi tafannin wasa bani da yanda zanyi dole ina mishi ina hawaye, wi don rashin imani irin na ya umar sai cewa yayi hakan yana burge shi domin ina yin kyu da kuka haka har kusan sati 2, sai dana saki jiki kan cewa ya barni sai yace shirya zaije kd yaga yanda marhaba suka tsara gidan nan da kaya ko ya yi kwana daya zaiyi sbd jibi zasu yi tafiya da faridarshi, kuma kila suyi sati 2 kofi da murna ta nace o ka barni can mana saikun dawo? yace to amma bri dai na gani inna samu yanda nakeso sai in barki din nan na shirya muka tafi.murna momy tayi da ganina ballantana yanda taga da ya umar yace kazo zanyi da sauri ga zatan ta yanzxn na som son shi ne n ko kan Sharadi nake duk dayace sai randana bada kai zan soma zuwa skul, ya di gamamin komai kuma sun bani lecture din da nakeso. da dare ina dakn anty saikumanace bar na shiga gurin su mama banje ba, amma an kaimusu tsaraba, anty tace kije ku gaisa, shi dan gidaba ai ya shiga dazu ko da dai yace min kila nan zai barki nace don Allah kisamin baki anty ni abj nan ma bana sonta dama yabarni tace zan mishi mgn amma kemaki dinga binshi dalalama,kinsannamiji dan lallashi ne nace to na fita nace da momy barinaje gurinsu mama nan na samu hadiza tazo muka zaunamuna ta hira can wayata ta soma ringing na daukaya umar yace kizo na jiranki,nce to na dubi su hadiza na danyi tsaki har suna hada baki gurn tambayar menene? nace ya umar dinnan ne muna hirar mu wai inzo mama tace shi nekikemishi tsaki? nace bafa dashinake ba, na tashi su hadiza namin dariya wai dole na amsa. kiran miji. aisha kam cewa tayi I. kin kowa more mihi anty asma'u na tafi na barsu suna hirar kyau da halin kirki irin na ya umar na tafi ina gungunai ni ina ruwana da wani kirkinshi tundani zaman wa'adi nakeyi dashi lkc yana cika zan kama gabana. A dakin momy na sameshi ya zauna rashe-rashe suna ta hira na kula wannan zuwan momy tafi sakar mishi fuska, ina shiga da sallama suka amsa ya mike yana fadinmomy gatananbarimu tafi tace to sai da safe Allah yasa rai kayimawa kasanjiyamunje da antyka da maman taku da su umma mun ga gida bayan su liyu sun gama walima, yace ai shiyasanace ma alyusu sa ayi karatun alqur'ani a ciki sannan suyi walima ba sai dole inanan ba, kaina ya daure nace kenan sabon gida zamu kwana? a raina mmy tace 'yatamu tashi lfy,nace tomuka fita ya shiga gurin anty yana mta sallama, tace to Allah yasa a shiga a sa'a ,yce to anty kimin addu'ar smunbaby, tace nasha alwshin daranyau kukan ka zan kaimaubangiji har mun soma tafita yace a nayi mantuwa ya koma yace anty ki aiko mana da break da saafe, tace to saida safe.ni kam banso ba, cikinmota ne yace naga duk kin damu kamar baki san zuwa sabongidn? umnace a raina kai sabongida ya dama gidan ya tsaru fiye da zaton mai karatu masha Allah haka nake maimaitawa duk da dre ne mun zaga ko'ina na gidn domnga hasken fitilu tamkar rana, ya nuna min dakna,muka shiga gaskya ya tsaru daganan muka nufi nashi, wow nace a A raina wani gado ne dan kasaritaly mai shegen kyau, dakin ya umar ya tsaru muka dawo falo na zauna shi kuma yace yana zuwa kallon tv nake yi. wanda shi knshitv din a jkin bango yake,kallo ya dauke min hankali shi kan ashe unguwar sarki yaje , sai gashi da kaji kilishi da kuma fresh milk ya zube a gabana,nace ninakoshi fa, yace Allah kizokici kada ki manta naki tone, inko kin kiki rusa lissafnki. yau m kwana naw ne da fara aikinki? yafa da cike da tsokana nace dibi sati 3 yace to ma zazo kici kinji asmy? ya yago cinya yazo yasa min a bakina, na amshe hak muka ci muka sha fresh milk kusan shadaya yace zo muje mu kwanta, yau ya umar shi da kashi ya cire minkomai danayi dan mots sai yace nifa taimaka miki zanyi ki samu kiyi karatun nan inkin fasa babu dole kuma kada kiyimin kuka, kai ya umar akwai bakin wayo, da haka yayi ta min wayo yana wasanni dani har ya shiga yimin wani salo da hankalna ya soma daukewanimana somamshi wasu daga cikin wasannin dayake koya min canhankalna ya dauke sainaji yana addu'ar saduwa da iyali donneman tsari daga shadan, kafin na ankare harya dauki hanyar daya jima yana kwadayinbi, nayi kokawar kwacewa na kasa ihu da cizo duk a Duk a banza da lama dama ya shiryama yau dinnanbai barni ba saida yamai dani mace sosai sannan ya soma lallashina,kai cewa yaso ya binia hankali ne ban tsaya ba, nikamkuka nakeyi sosai kamar wanda uwarta tamutu, ba kukan zafi nakeyi ba ba kukan bakin cikn kau min da budurci nakeyi naso n gama karatuna sannan na samu wanda nakeso sai inkai mishi budurcina amma yau ga wani mugu ya same ni abanza a wofi. da kanshiya min wanka yana ta lallashi na yacena iya wankan tsarki? tamkar in haushi da duka , namishi gatse nace ban iya ba, shine ya shiga koyamin nayi bnza dashi ya fita yace kiyi bari in canza zanin shinfida,was wasa nanbar mu mun runtsa ba, kwana nayi ina kuka sai kiran sallar farko sannan wani wawanbarci ya daukeni shi kuma ya tashi yayo alwal ya shiga jero nafila har zuwa lkcn da aka shiga masallaci shima yayi sannan yazobakin gadon ya zauna, kallona yakeyi wan so mai tsanani ykeji yakai hannu ya shafi kumatu na ga idona sun kumbura sbd kuka tausayina yakeji ya sani harga Allah nasha wahala saidai shi kam yana cikin farinciki tare daannushuwa, rokonshi daya Allah yasa kwallonshi ta shiga raga. Da safe yake son wucewa ammaji yake tamkar kada ya tafi ya barni ina mabai sanar da farida tare da ita zaije ba da ya tafi dani, ya gwangwaji amarcinshison ranshi. haarya gama shri ban farka ba farida ta kirashi tanacewa sun fsa tafiyar ne? tace yana zuwa zai ma biyo jirgi ne direban sumomyya iso dauke da kayan karin kumallo, nan take yace da direban yajuy yazo mishi da antynsh. sai gasu duk a tsarace take nasu zaton babu lfy, momy fadi take Allah yasa ba wani rikicin bane dama 'yar gidan tawa jiya nakula bataso tafiya ba,har sanda tazo ban farka ba, yace anty na yi barnane, 'yar gidan momy gashi da kokawa komai ya faru,kin ganta nan kwana tayi rigima sai asubahin nan sannan ta runtsa, shine har yanxunbata farka ba anty tace ikon Allah,muka yita zargin yrnyr nnkusan har yanzunsu mama basu warware da fushn da sukey da ita ba, yace shyasa na bari sai anan danki sani na san bai dace ku sani ba . amma sbd ta fta daga zargi ne. anty tayi dariya sannan tace Allah yasa first nyt mu samu baby yace amin antyna, xan tafi domin sha biyu ya kamata muna edo state, shiyas zanje n dauki my farida mu wuce, don Allah ga asmy ki lura min da taplease, 2wks kurum xanyi amma zan dinga kiranta tace tana ganin xan zamu koma da ita, ya tsuguna ya mannamin kiss a kumatu, sannan kan lebunana, anty tace a gabana? ya fita yana darya,tace Allahya tsare. [7:42PM, 17/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu 2----8 Sanda na farka banga kowa a dakin ba,nayi miqa jikina yayi tsami, sabon kuka na saki, anty ta shigo ta kama ni,miqe asma'u nace nidai dan Allah anty kuce ma ya umar ya sakeni bana sanshi na tsane.... ta katsa ni tare da rufe min baki haba mana asma-u baya gaya min kunyi yarjejeniya ba? cikin kuka nace munyi mana amma ba xan iya ba bana sanshi,tace to kidai yi shiru na ce, taje ta hada min ruwan xafi na gasa jikina, nayi sallah na shafa mai idona luhu luhu.anty tayi waya ta sanar da momy,domin shi ko da ya biya baice ga abinda ya faru ba, cewa kawai yayi bani da lfy ne, a gabana anty tace momy komai.sai gasu jamila da nafisa momy tace suxo tayani xama ko da anty ta dawo gida.da kyar anty ta matsamin na dan ci wani abu.yinin ranan sai kuka nake yi anty tayi lallashin har na soma bata haushi ta gaji tace wai ke kukan me kike yi ne?sai kace kece mace ta farko da ta soma kah budurci?ai duk wata mace dakika ganta in dai ta kai yar mutunci to ta ketara wannan siradin. Jamila tace kinata faman kuka ko mutuwa aka miki ai sai haka,nace ni wlh dama mutuwa nayi da wannan baqin cikin Allah ni bana san ya umar.jamila ta dubeni cikin jin haushi tace to kada ki soshi din man ke dan kin samu ma ya aure ki? wlh ya umar ba ajinki bane,ke da kanki kin sani, taja tsaki ta fita.nafisa ma taji haushi amma bata yi magana ba, anty ta ce xaki ja ma kanki matsala da ya umar mijinki,ni xan tafi ga sunan su xauna tare dake. ta tafi su jamila falon qasa suka xauna ni ko haka na yini ya kira waya har ya gaji naqi dagawa.sunyi waya da anty ta mishi bayanin yanda na daga hankali na,yace naqi ma na daga wayarshi,amma bari ya tura momy itace kurum yasan xata shawo kaina,dab da magariba sai ga momy ina ganinta na fada kanta ina kuka sai lalla shina takeyi,jikina ai dama tuni ya dume da xafi nan ta aiki su jamila da direba sayaen magani,su jamila haushina suke ji sbd bana san yayansu,sai da aka kwana uku sannan na wartsake,dangi sunata xuwa gaida ni tare da ganin sabon gidanmu. Rahma randa taxo mun kule cikin daki ina kuka ina gaya mata wuyan da nasha, ita kam na lura hakan ya mata dadi,domin dry ta kama min nace rahma yanxu kin canxa kin daina sona,tace san kenan asma'u,domin duk mai sanki xai miki murna, haka nan kin xama abin alfahari gun mijinki, na harareta nace Allah dana san ya umar ne xai maida ni mace dana raba ma gayu tun a titi.dry sosai rahma ke min na samata Allah ya isa, tace dama ai ishesshe ne. sbd yanda dangi ke shiga da fita gidanmu,sai gashi har sati biyu din ma tayi.aranan da yamma dab da magariba sai gashi ,lkcn muna kallan MBC2 nida su jamila. yayi sallama da muryarshi mai cike da dadi, su jamila duk suka shiga taitayinsu daga srtn da muke yi,ya tsaya daga bakin qofa, na gane nufin shi, waton inxo in tare shi domin a abuja haka yake yi in nice dashi ya ganni nan xai tsaya sai naje na tare shi.na miqe babu na nufe shi, ciki ciki na mishi sannu ya kamo ni ya rungume to nauyin su jamika bai ji ba,na amshi jakar hannun shi da sauri nayi gaba. Shi kuma ya tsaya gun su jamila yana amsa gaisuwansu. bayan isha yana cin abinci, ina xaune kusa da shi sbd mugunta ya barni inje gun su jamila muyi kallo yaqi wai saidai in xauna ya gama kawai,dole muyi hira, yana gamawa yace bari nakai su jamila gida in dawo dama banje can ba nan na xarto nace su jamila fa nan xasu kwana,tunda a dakina muke kwana,yace to yau dani xamu kwana kada kixo ki min ihu suna nan,na xunbura baki, yayi dry.haka ya tafi ya maida su jamila kafin ya dawo na kulle qofata nace baxan xauna kaxo ka min irin na rannan ba, na soma bacci naji an dauke ni cak, na saka ihu ya dire ni yana dry.mai tsoran tsiya kin rufe min qofa ko? to na bude, ya jani sai dakin shi ganin take taken shi na soma kuka,yana lallashina ya ce yau baxaki ji xafi ba, ya umar yaran kan soyayya haka nan ya san yanda xai yi ya mantar da mace ko ita wacece,lkc qanqani ya rame ni,wata rayuwa mukayi ranar mai dadi,sai daga birani na soma kukana, bana sanshi yayi ta lallashina hakan nan muka idar da sallah asuba. Ya umar ya soma min wasannin na ce gsky bana so,yace to amma ai munyi yarjejeniya neko? ke dai naki to ne,nace amma ai ba ace ko da yaushe xaka dinga min wannan abin ba, yace inji wa? matata gonata ce haka manxm Allah yace, tunda yanxun kina matsayin matata ne ai dole ki yarda in xo miki ko yaushe ne.yan magana yana kallona yana murmushi. kwananshi 2 yace to mu koma abuja in fara xuwa mkrnt,mumje munyi sallama da su mama da momy muka nufi abuja. cikin sa'a na shige jami'a inda nake krtn mass comm. xuwan farko shine ya kai ni yasa joseph suje su dauko ni sai farida ta nuna rashin jhn dadinta inda tace haba sojana, ba gani ba nima fa mkrnt nake,ko ba xanje ba ai xan kaita, yaji dadi sannan yace min to mu dinga tafiya da faridarshi,ban so haka ba sbd nasan wata rana sairai ya baci, haka nake kallan su suna xuba soyayya a gabana, ni kam ban damu ba tunda ba wai ina san shi bane,in yana dakina kuwa sai nasha lallashi tare da dadin baki kafin in yarda dashi abin da yafi ban haushi . Kullun sai na mashi kuka yayi ta lallashina yana cewa kada in damu tunda ba dindin din xamu xauna ba. yau muna da lecture qarfe 2 dan haka nace ba xan je nayi ta xama ba farida ta fito ta ganni xaune, cikin isa ta dube ni inxaki jene ki taso inko ba xanki ba in tafi. nace mata ni sai 2 nakeda lecture tace kyaji dashi ta tafi nace kodai kinji dashi,2 nayi nayi shirya na tafi,na samu drop xuwa mkrt sai shida na taso. ina kallanta suka wuce da wasu qawayanta, ta ganni bata ganni ba oho, na kuma samun drop xuwa gida,sanda na shiga an idar da sallar magrib. farida tana dinning sallama nayi bata amsa min ba nan na nufi dakina,sai da nayi wanka nayi sallolina sannan na fito ,lkcn ya umar ya kira wayata,na duba naga shi ne sai naci gaba da tafiya gun su,domin na san dama bai wuce yace inxo muci abinci ba. na xauna tare da fadin sannun ku. ya umar ne kadai ya amsa,cae bayan an fara cin abinci,sai farida ta soma magana, yauwa sojana,dama ina so in maka magana,yarinyannan ka gaya mata,ba kimar ka bane tana Farida tace ba kimar ka bane tana irin wannan gidan sannan ta ringa hawa motar haya. ya ajiye cokali ya dube ni motar haya kika shiga asmy nace eh, yace sbda me? fuskata adaure nace sbd bani da mota, yace ban gane bakida mota ba baga my farida kuna tafiya ba? nace to ni yau 2 xanje ita kuma kullun da safe take tfy yace me xai hana kimin waya gasu joseph sukai ki? yace gaba bana san hawa motar haya ko acaba,duk sanda kika sake xan bata miki rai,farida tace shi yasa nace bari in gaya maka a gaban ta sbd kada ta xata ko munafinci ne, da tace min 2 take da lecture da ban musu magana sun kai taba?yace ko ita ce tace su kaita xasu kaita, kallan farida nake yi cike da mamaki na fa gaya mata tace naji da shi lallai ma matan nan.jin suna ta faman min fada yasa na tashi na nufi daki na bar abinbin na kulle qofata. na fada kan gado ina kuka,waton shi baima san dole nake xaune bane da xai tasa ni yana min fada? Ita kam farida hakan yayi mata dadi sai ta qara da cewa, kenan dan an gaya mata laifinta shine na fishi? kaga gashi harda barin abinci jeka lallaso ta ,shi kuma sai yace dan allah ki barta dama dan taga ina lallabata ne shiya sa take min salo ki barta kada taci ba cikinta xata kai ba?da safe ban fito da wuri ba sbd yau ma sai goma nake da lecture ina jinsu suna break dan farida tace sojana bari in kira qanwata ta karya ina ganin har yanxu bata huce ba, yace qyale ta kawai. ta miqe aiko da kissa bari dai sojana in kirata kasan yarinya ce bama kulata ba,ina kwance ta shigo sai da ta qare ma dakin kallo sannan tace lalle an xuba kudi a dakin nan, kuma dan wulaqanci irin kayana, ta dube ni ke kuma mara kunya kina nema ki dauke min hankalin miji xaki san kina kishi da yar barhki, babu boka ba malan tsabar tungu ma ya ishe ki, na dube ta na ce tuggun ki xai qare kanki kuma baxan gaji da sheda maki cewa mijinki baya gabana ba, dama xaki roqar min takardan saki kaf 9ja bani da kamarki. Na tashi na sauko daga gadan nace mijinki shine ya liqe min ko a gaban shi xanfada ta daga murya dan ya jiyo,ni kike ma ihu? daga xancen arxiki? nace an maki? haka ake xancen arxiki? tace kada ki xageni, ya umar ya shigo rai bace my farida ba sai dana ce kada ki xoba, kin san yarinyar nan bata da kunya,ga mamakina sai naga ta soma kuka,tana fadin yarinyannan dai kasan da ace ina da qanne nayi qanwa ta kusan hudu da ita ko? shine daga xo ki karya sai ta hau ni da baqaqen maganganu har dace min ka liqe mata ita bata sanka da sauran surutai,ban da taci arxikin ka ba sai na lallasata ba? ya jata ya rungume,yi shiru my farida,ki barni da ita,ni ko banxa na masu nama shige toilet na tsiri wanka, suka fita yana lallashinta sai cewa tayi ya wuce amma ka dinga mata nasiha ita rayuwar dny guda nawa ce yace na gode my farida shi yasa nake qara sanki Allah ya sani ina girmamaki sbd tsoran ubangijinki ta rungu me shi tana gdy. na fito wanka ina shafa mai yayi sallama ciki ciki ,ya shigo Ban ko amsa ba du da nasan mahimmanci sallama ya tsaya yana kallona, yi nayi tamkar ban san da mutum ba, yace wai asma'u me kika dauki kanki? nayi banxa shi yace dake nake magana, kina nufin yanda kike so xakiyi? to kinyi kadan kuma ruwanki da matata,duk abin da xakiyi ya tsaya kaina tunda ni na kawo ki ya juya ya fita,nace kudai kuka sani domin babu mai takura min cikinku goma nayi na fito sun fita ita da shi sannan basu joseph sai jorn maigadin gate na ce mishi ina su joseph? yace madam babba ta aike su suleja,nace wani abin xata kulla kuma xai qare mata, na tafiyata mkrnt drop dindai da ba aso na kuma dauka hakan nan da xan dawo duk daba fanni daya mukd da ita ba nasan da xan dinga ganinta amma bana ganinta ban da jiya, bayan nataso misalin 2 da rabi kai tsaye na samu drop na nufi gida yau nice dashi nafito,da irha na gyra muru gun cin abinci,na koma dakina agun cin abincin ne yake tambayan farida ina nike? [7:44PM, 17/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu 2----9 Ta sheda mishi ina daki ya kirani da kanshi harda cewa ka lallashe ta domin bataso ina mata mgn dazun nan ina skul lkcn zuwanta yanayi da yake na aikisu joseph suleja, sai na dawo dan na dauke ta na kai ta skul gaba da gaba tace min ita da shiga motata har abada kuma motar haya yaanxun ta soma shiga duk yanda xamuyi muyi da sauri ya dube ta, yau ma haya din ta shiga? tace haya mana ta shiga amma don Allah kada ka saurare ta ko mata fada shiru yayi yana tunanin me zaiyi akan wannan yrnyr. ya mike ya nufo dakin a lkcn ina zaune bakingado ina tura ma mina text ya shigo rai bace yake,cike da masifa yake fadinke wai ina tambayarki, me kika daki kanki? ban za nai miashe ranshi ya kara baci ya fisge wayar ya jefar kan gado, ke 'yar raininhankali ce ko? na mike duk da raina cike yake da tsoro kada ya dakeni sai da nace, to me na maka? yace oh ba kima sani ba ko? wato danace kada ki kuma shiga motar haya dankin raina ni shine kika kuma shiga ko? nace yaya ba zan shiga ba tunda bani da mai kaini kace na bi sujoseph su kaini ta aike su sannan ita kuma tayi tafiyarta me zan mata?yace kada kimin karya ko ki tsaya kina tsara min zance. wlh ba zan dauki rashin jin mgn b, haushi ya kama ni nace to wai an daure maka ni ne? yace toh kin ma tuna min dama na gayamiki muddin kika karya doka dana sa miki to sai mun sake sabon lissafin kwanaki, don haka sai kisa ke sabon lissafi daga yau Bansan snda na saki ihumai karfi ba, har farida ta zata dukana yakeyi donhaka ta shigo cike da murna tana fadin haba sojana, me yayi zafi haka hrda duka? jinkalamn dake fitowa daga bakina yasa tayi turus nace wlh ban yarda b ai sharadin naka bakace zaka tasani kana min fadaba, to wlh ka bani takardata na fasa sharadin duk ma abin da za'a min a gidan amin, inma sunce ba zan zauna gidajansu ba ai gari da yawa maye ba zai ci.... saukar mari naji tayau, na dafe kumatuna, ka mare ni? wlh bazan yarda ba, yace to zoki rama. farida tace haba don Allah sojana, yaya zaka kula taa kema rshin jin mgn ne....da sauri nace kada ki dame ni ke kuma duk bake ce me sawa ba, Allah zaimin maganin ki ya juyo kada ki saka ta cikin shirmenki, zan hukun taki domin ba sa'arki bace kuma tana da kima a idona, bakina bai mutu ba nace da kai da ita bakwa gabana,naci gaba da kukana , suka fitana tashina soma hada kayna ina zubawa cikin akwati na. shi kam daya zauna dan cin abincin sai ya kasa, daki ya tashi ya shige ranshi sam babu dadi zuciyarshi ta shiga zargin shi da rashin kyautawa domin tana ganin asma'u wata abin sontace gami da girmamwa, don haka tana bashi shawa maza ya tashi yaje ya lallashe ta nn take yabi umarnin zuciyarshi ya mike ya nufi dakin a lkcn ni har na jawo gyalena, ina kuka naja akwati zan fita mukaci karo ya rungume ni yayi cikin daki dani ina kokarin kwacewa yace haba asmy yi hkr ban kyauta Tsam ya matseni yahan niko motsi sai shfa kaina yake yi yana cewa inyi hkr in daina kuka, nace a'a ni dai yau gida zan kwana bazan sake zaman gidannanba, yave nasani naki sona amma ki kara hkr ina mki wasa ne da nace na janye sharadin, ban janye ba yana nan yu wata daya ko? da sauri nace a'a wata biyu da kwana tara yace a'a'a ashe ma munyi nisa to shi kenan kin gama lkcn yayi nisa, sannan skul zan kai ki da kaina kafin in samo miki direba wanda shi aikinshi shine ya kai ki skul, sannan yaje ya dauko ki bayan kun tashi, haka yayi ta lallashina tare da kwantar min da hankali har na daina kuka, na yarda zan cigaba da zaman sharadi. sannna ya umar yayi ajiyar zuciya tare da cewa nazo muje inci abinci. duk wannan abin yana faruwa ne kan idon farida wanda ta tsaya tana leke ta kafar makullin dakina, tasha mamaki kafin ta nufi dakn ta zuciyarta a bace lallai sojanta ya soma shiga tarkon son yrnyr nan kamar yanda ta dade tana zargi ita a yanxun ta isa ta mishi masifar da yrnyr nan tamishi dazun bai casa ta yaci kaniyar ta ba wata zuciyar tace kenan yafi sonta dake? Gabanta ya fadi laillai dole ta dauki mataki kan wannanlamarin, dakina ya kwana sai dai duk kalatar shi dole ya barni domin nki yarda san shiko lallaba ni yakeyi. dare ya ratsa grin shiru, ya umar zaune kan sallaya yana kaima Allah kukanshi yana son ubangiji ya sanya matarshi asma'u taso shi kamar yana ya jarabci zuciyarshi da sonta domin yanzu wani so mai zafi yake shigar ta duk wasu kofofi gashi na jikina, rayuwa mai juyi kanam yau ya umar ne ke rokon Allah yasa asma'u taso shi. da safe duk saurin da yake sai daya jirani8 tayi sannanmuka tafi wanda hakanbai ma farida dadi ba, kuma har ta nunamishi ta hanyar kissar dta iya , tace kenaka raina kulawar danake yi kan asma'u? shi kam yacce sam ban raina baa, inason dana mata abu zata hadani da momy kiyi hkr nasan kina iyakar kokarinki da ita, shiyasa nake kara sonkimy farida, da wannan kaiman ya rufe bakinta.ni kam kafin sati ya zagayi kullum zai kaini skul sannan zai koma ya dauko ni cikn satin ya kawomin direba wanda shi aikinshi kawai shine ya kaini suk, sannan yaje dauko ni koaike ne nice kurum zan aike shi sunan shi balarabe, kym dan kd ne, yace iyayen shisuna hayi, haakan bai ma farida dadi ba, domin waya ta kira hafsa lady tana gayamata lady tace kada ki damu kan yrnyr tunda ita kan ta kince ba sonshi take b, shima bki da tabbacin cewa yana sonta donhaka kicigaba da yimata kissa in bai yiwu ba saimu hada da malamai. Farida tace shi kenan ,yanzu yaya batun super market dina nan yola kasuwancin yana tafiya kuwa? lady tace yana tfy mana, kin samu shagon da kke son budewa na nan abj? faridatace wlh ban samu ba kuma kin san a boye nakeyi banaso sojana ya gane,kin san zaice ina na samu kudi? lady tace ki hada baki da yayarki ta nan abj ba sai kice na tane ba, farida tace tun yaushe anty yaushe anty suka bar abj, suna lagos yanxun ina jin ko wata banyi a abujan nan ba suka tashi yanzun dai ina tunanin in gaya mishi amma sai ince shi zai bani jari ko yaya kika gani? lady tace kwarai haka zaki yi in yaso da komai ya kankama sai ki fito da kudi ki jibga kaya a shagon cikin siyasa farida tace haka ne domin kina ganin mutumin nan shegen kishi da bin diddigi mota fa na siya henesi sabuwar kira,amma na rasa yanda xanyi in fito da ita tana gidan shakatawar alhj jamilu lady tayi dariya tace sojanki sai ke . Yau kam da safe ina kicin ya smenicikin shirinfita yake,yace smy xnje calaba yanxun nanina zuwa ofis na samu n tura mu wani gwajizmuyina2wks pls ki sakanicikin addu'a ,ya shafi kumatuna sannanyace sai na dawo, bance mishi komai ba a raina cewa nayi kada ka dawo, bayan tafiyarshi da kwana 1farida mata kara gaba abinta, africa ta kudu sukaje ita da alhj jmilu.gida daga ni saini ban damu ba, domin ina zuwa skul kwanta 8 ta dawo, shi kam satin shi 2 ya dwo babu dadewa aka soma azumi cikin azumin nan mabaya zama yau yana cangobeyana can, har sallah ta kus sauran kwana 11 yacein shrya yakaini kd, sbd zsujeummara shi da farida koa jikina dominnilkcnsharadinmu yancikin 6month burina shineingayauya umar yasake ni.farda cemai rokon aje dani yace tabari ni sai inje aikn hajji. Inajin sanda muka is kd yana fadama momy a gabana wani niakinhaji xanje ,a raina nacebabbar hajina kaa saken. naso in zauna gurinsumomy tcea'a tunda gagidana muje dasujamila harda nafisa da kuma aisha gidanmu, wani sabon al'amari tunda nazokd kamar da ciwo na iso zazzabi ciwon kai,daga nan saikirji ciwoo yayi yawasu jamila suka gayawa momy tazo yace in shiryamuje asibit, da yake harda bala direba namuka zo ks sbd duk inda zanje ya kaini momy tsa su jamila suka kira shi a waya ,don yazoya kaimu. diamond hospital akai kaini gado suka banibayan bincike bincike suka tabbatar da cki wata 2 a jikina bakinciki ya saka ni kuka, momy kan farin ciki tarungume ni tana cewahaba asma'u menene abinkuka? wannan ai abin farin ciki ne cikinkukanake fadin, don Allah momy kisa a cire min wlhbanasoncikinnantace ki daina fada Allahyayimkikyautasannn kice bakiso?haka tayi ta lallashina har nayi shiru, kwananmu 2 muka dawo gida ban koma gidana ba nan na zauna gurin momy ,murnaa. gurin abbba sai kace bai taba samun jikokiba sai kan cikin nan antynshikuwa aitafikowa murna duk abin danace inaso shi zanci mama ma wannan karon har ita ce 'yan zuwa gaishe ni sannanta nunamin yanzu tanayi dani domin sanda tazo nace ma momy ina zan samu dan waken dawa? tace in bari za'a kawomin haka taje gida ta sa akayimin. Antynshi ce tayi mishi albishir ranar ina kwance kan doguwar kujerarta ta kra su suka gaisa dashi ke tasa waya inaji yana ce mata ina a amanata? hope tana lfy? tace kwarai lfyr ta lau,yace bana samun wayarta dukna damu,anty. asmy tana da rigima sosai gashi yanzun ta shiga rayuwata sosai amma ita bata sona, anty ta kalle nicikin murmushi sannantace yanxun ma na kiraka ne in maka albishir yace dabino da zam zam ina jin ki, tace mun samu karuwa yar rgimarka tana dauke da juna biyu don haka sai ka siyo mana kayan beby yanda ya rikice a waya abinhar mamaki ya bani,fadi yake don Allah antynah da gaske? Alhmdl anty zanje inyi dawafi zanyi sallah in gode ma ubangijina,sannan inrokesi ya sauke ta lfy, don Allah anty kice mata ta bude wayarta, zucyata tanamatukar son jin muryarta, ya kashe wayar. Farida ya isko tana cikin daki tanata sheka bacci tafi mai da kai ga bcci fiye da aikn data zoyi, ya rungume ta sannan ya girgiza ta yana fadin tashi my farida kiji abin farin ciki daya sameni, da sauri ta tshi ga zatonta training din da yaketa addu'a Allah yasa yana ckn wadanda za'a tura ne ya samu lbrn sunanshi yan ciki,tace menene sojana? yaceasmy tana da ciki ,haba wani mummunan faduwar gaba taji nan take kishi ya dirar mata tamaimaita kalman ciki? yace wlhyanxunnannty nah tayo min way, tayi kokari ta danne kishinta tace Allah ya bamu masu albrka, yace amin.hakika ya jima yana rokon Allah ya inganta mishi ya kuma roki Allah ya cusa sonshi a zuciyar asma'u da sukazo batun tsaraba kuwa nan farida taga hauka, kaya yayi ta lodnamata da maza har sai da tanuna jin haushinta sannan ya lafa takano suka sauka kaitsaye kd suka nufo a jirgi lokacin ina bacci cikin baccin nake shakar kamshin wani daddadan turare, sanda na farka sai nagaya umar sanye da fara jallabya kara kar Da hula itama fara sai yayi minkama da larbawa, domin sajanshi yayi kama kawai dasu , ya umar yana da kyau namijine cikinmaza, yaana cikinmaza masu wuyar samu,irinsu ne one in town amma a zuciyata ba sonshi, kamshin turarensa yayimindadi yasaki murmushi sannan ya zauna kusadani ya dubimomy cike da fara'a tafarka,momy taceka tshe ta dai ya tsura min nikam kamshin turerenshinake shaka ji nake tamkar in tashi in shigejikinshi inta shakar kamshin momy tace ina farida fa?yacetanadakin anyna ta mike bari insaantyn taka ta shirya muku abinci ko? taana fita ya dube ta da murmushi ni kam har da kra shigar da fuskata tsakiyar kirjinshi kamshin nan ina sonshi shi kam yaji dadin yanda nayi lamo a jikinshi ya saka murna kuma yanazaton Allah ne ya amsa addu'arshi na fara sonshi ne tunda yaga in ya rungume ni tureshi nakeyi ko in ta mutsu mutsu amma yaunice da kara kankame shi, bmu sanmomy ta shigo ba saimgnr ta mukaji tana cewa, farida shigo mana da sauriyaa sake nini ko sbd kunya sai na koma na kwanta shima ya dan sosa wuyar shi irinna wanda yaji kunya din nan, sannan ya zauna . [7:45PM, 17/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu 2----10 Farida ta shigo muka gaisa tace yaya jiki?nace jiki da sauki na dai ki tashine ya samu tafi tare ko dankaratuna ammaa naki yarda,nace ni gurin momy zan zauna momy tace ya brni , ina kara warwarewa sai yazo yaa tafi dani, yanda farida taga kowayana lallaba ni musamman shikanshi sojan ta hankalinta faya tashi sannan ta soma tunanin ciki itama suka tafi bayan ya roke nikan cewa kada na kashe waya na barta a bude domin yana son jin muryata ,har ma yace yana tayi ni murna, mun kusan rabuwa cewar shi ina haihuwa zai bani takardata,hakanyasani murmushi donmurna. bankokashe wayata ba kamar yanda yaroka, sun isa ya kirani asmy mun isa gida da fatankna lfy dababyna?nace um yace ki dinga min mgn mana,ni dai shiru namishi , yace toki shafa min baby na na tura baki duk na kosa yagama mgnr ,kamar ya sani yace to shi kenan sai anjim. na riga shi kashewa, sannanna kwanta wanina me cikiwai yanzu babu abin danakeson ji irin kamshin ya umar, hak na kwana da safe mana samu turarukana inata shaka amma daga wanda yakusan amai saime son sani ciwonkai donhakana tarkata su na'aje kayan da na cire na daukana kara shakar kamshin. Yau kwanan shi 3 da tfy cikin dare na kasa bacci, qamshin turaran nan nake matuqan so na shaqa,nunfashina har yi yake tamkar xai dauke,kunsan mai ciki in taso abu ga kayan da ya rungumeni dasu neke dan shaqa momy ta saka su cikin wanki an wanke su an goge na dauki wayata na shiga neman layinshi wani abin haushi saida ta soma ringin sannan wata xuciyar tace me xaki ce masa? nan take na yanke sannan na koma na kwanta.shi kan lkcn yama kan sallaya yana miqa godiyarsa gun ubangiji ta wannan baiwa da ya mishi, bayan ya kammala ya miqe sai daya xauna a bakin gado sannan ya dauko wayarshi dake aje gefen gado ya duba ga mamakinsa sah yaga no ta da sauri ya soma neman layina,har na fara bacci naji ringin da saurh na duba shine araina nace me xance mishi? amma sai na dake na dauka, yace asmy me ke faruwa? nace name fa? ya qara saisaita murya yacf naga call dinki ne,nace ni kuwa?na dan ja tsaki gsky bani bace yace hope kina lfy.nace lau,amma kuma nayi shuru, yace fada mana me nene? Nace kodai ma bar shi,ya tausaya murya plx asmy gayamin mana, nace to yaushe ne xaka xo? yace cikin sauri kina san gani nane? nace a'a dama xance ina san turare ne nawa duk basamin dadi yace shi kenan xan xo miki da shi cike da haushin kana na kwanta a raina ina cewa qilan ma ya xata na damu dashi ne.shi kan cike da farin ciki ya kwana xuciyarsa ta rage xugi yana ganin ta soma damuwa dashi.sati daya da yamma lkcn mun gama dramer dasu jamila xata dora shinkafa da miya nace miyar nafi san asa ganda maimakon kifi da nama xa-a sa,momy tace to maxa jamila taxo jaje kasuwa ta siyo ganda, haushi ya cikata tace wlh momy kina shagoba asma'u yanxu sbd ita xa'a canxa abin da akai ninya? momy tace ki dau kudi ki wuce banasan dogon turanbi nafisa dake nhnke kaya tace ai ita anty arma'u ta cika saka mutane aiki kamar kanta aka soma cikin sai dana bari momy ta fita nace kema yanxu xan qirqiro mikh naki.tace wlh babu abinda xan maki tunda yau bani ce da aiki ba,nayi dryr mugunta,momy na shigowa nace ... Nace nafisa ina xan sami xobo mara suga sosai? tace oho miki,momy tace baxa a rasa xobo anan gidan ba tashi ki hada mata nafisa,tace wlh momy dama tace sai ta sani aiki ne ba wani xobon da xata sha, na dake nace in baxaki yi min ba to siyo min gun maman walida,momy ta ce a'a ta tashi ta hada da yawa kowa yasha nafisa ta fita rai bace na shige bedroom ina dry.sai kawai na tsinkayi sallamar ya umar cikin muryansa mai saka mara jin magana natsuwa, na xauna gefen gado, naqi fitowa, take raina ya soma tuno min da daddadan qamshin turaranra ji nayi tamkar in fita in rungume shi,duk da rashin ran da nake mishi amma sai na dake,sun gasa da momy ta tambayi farhda yace tana gaishe ta,sun dan taba hira kafin ya tambaya ina nike? momy ta ce tana nan ciki yace ba wata damuwa ko? momy tace da sauqi damuwar nan ka shiga dai tana ciki ua tambaye ta, jin haka yara nayi shiqu tamkar mai bacci na kwanta, ya shigo da sallama yatsaya akaina yana kallan fuskata,ina jin sautin murmushin shi. Sannan ya tsugunno saitin kunnena yace asmy na sani idonki biyu,yanda ya kusanto ni sosai yasa qamshin shi ya kai ma hancina xiyara,na bude ido a hankali na sauke su fes akan fuskarsa, yasa hannuwanshi ya dago ni xaune shima ya xauna, ban ankara ba naji tafin hannunsa akan marata yaya bebyna? na runtse ido tare da daure fuska, sam bana san tuna cewa inada ciki, ya rungume ni tsantsan na qara nutsa kaina cikin qirjinsa qamshin shi nake shaqa tamkar naga turaren, ina qara manne mashi ya shafa ni a kunnena ya ke tambayata kina san babynmu? na girgixa kai alamar aa ya dan sausata riqona yana duban fuskata baki san babynki? na bata rai nace ni fa ba babyna bane,yace to yanxu ke ba kya sanshi kenan nace allah ni ba ruwana da shi, na miqe ina qoqarin qwacewa yayi wata sansanyar ajiyan xuciya sannan yace to ki kawo min wani abu inci, na fita shikuma ya bini da kallo a ransa fadi yace,sam batayi kama da mai ciki ba, ya qosa yaga cikin nata ya tsufa, tafiyan kasaita ta masu ciki tana birge shi. Tafiyan masu ciki tana birge shi,amma ita sai qirjinta ya ciko yayi dam, sannan hips dinta suka qara fitowa.wata sha'awa ce ta motsa mishi dama yayi mssng dinta da yawa yana so wasu halittunta.na dawo yace to xauna ki xuba min,ya kalmashe kan bapet nima na xauna ina xuba misii na tuna nace yauwa em ina turaren? yace ok yana gidanmu can gwamna rd, kin san can na fara sauka na manta da shi,yayi murmushi xa muje ki dauko ai ko?na kalle shi a raina nace shi wannan ya umar din ya cika wayau, a fili ko sai nace a'a in kaje ka kawo min. bayan sallar isha nayi mugun ci sbd miyar gandar tayi min dadi sosai ga kuma xobon da nafisa ta hada ina ci ina musu dry da gwalo jamila tace Allah yasa yau mijinki ya kwashe ki mu huta.nafisa tace Allah yasa su wuce abujan tare xaki be, waya ta ta soma ringin na dauka ya umar ne nace slm alkm,ya amsa da kema amincin Allah ya tabbata agare ki, asmy shin kina buqatar turaranki? nace eh yace ki same ni nan qofar gida cikin mota, na tashi ina neman mayafi,momy tace ina xaki? Nace ya umar ne xai bani saqo,nafisa tace ba wani ke dai sai da safe. jamila tace ana san miji amma ana kai wa kasuwa, tsaki kurun na musu na wuce, momy ko dry take mana,xaune a maxaunin drb yace shigo mana ina shiga yaja mota muka soma tfy nace ina xamu jene? yace gidanmu ki dauko yanxu nan xan dawo dake, nace ban fa yi shirin fita ba,yace ai ba wani baqon guri xamu je ba gidan mu xamu je shiru na mashi.bayan mun tsaya ina qoqarin fitowa shi ya fito ya rufe gefen xamanshi ya xagayo sai kurum naji anyi sama dani haka ya rungume ni tamkar ya rumgume jaririya, da qafa ya rufe motar sannan yayi sama dani laf nani a jikinshi ina shaqar qamshin turaranshi.idanuna a lunshe dan tsabar mugunta irinta ya umar sah jina nayi cikin bahon wanka,cike dam da ruwa da sauri na tashi xaune tare dayin wata shegiyan ajiyar xuciya,shi kam dry yake min na saka mishi kuka,wanda ni kaina na san na tabara ne.ya soma lallashina wai bari yayi min wankan,banxa na masa ya cuda ni ya wanke tamkar jaririya. Ya nado ni cikin tawul, ina mamakin ya umar in yana soyayya tamkar a india shi yasa wani lkcn ban sani ba nake biye masa sai daga baya inxo ina jin haushin kaina. kan gadon shi ya sauke ni sannan ya warware tawul din ya barni wai xai shafa min mai,daga shafa man ne ya xarce da min kalolin wasannin shi masu sakani cikin shagala, kada kuga laifina bansan yanda xan fassara maku ya umar ba,bangaran soyayyar auratayya, da ace ina san ya umar to dana ce babu wanda ya kaini dace kaf fadin duniyar nan, yana sani in mance so ko qi in mance k6ai da kowa nakan dauka duniyar daga ni sai shi aka halitta,lkcn da natsuwa taxo mana sai ma rinqa jin takaicin kaina ni da ba sanshi nake yi ba me yasa xan ringa biye mashi, shin na manta wulaqanchn da ya min can baya? shiko dadi tare da farin ciki ne ya cika xuciyasa yariyan tana da bahwar ni'imar da ba kowace mace ce take dashi ba, sannan ya san dama mace mai yaron ciki abin bukatar kowane namiji ce sbd wasu dalilai, cyan haka tana gamsar dashi. Da asubahi kam naji haushi sosai sbd yaji qe min kayana gashi ba dakina muke ba babu kayana kuma a dakin shi jallabiyarsa mai gajeran hannu ya bani gashi ta min tsawo cikinta nayi sallah ina ta fushin me yasa na biye mashi nan ya kuma lallaba ni har da cewa in tausaya mishi da fa na haihu shi kenan, xai bani takarda, nan dai nuka sake lulawa ,da safe anty ta aiko mana da break nace ya kamata mu soma shirin komawa gidansu momy tunda nifa banma xo da shirin kwana ba, yanxu ma kunyar momy xanji, yace menene na jin kunya bayan gidanki kika xo kuma tare da mijinki kike,nace mijina fa kace mijin sharadi? yace ok yes haka ne,amma yanxun sai yamma xan tafi na fasa tafiya da wuri shiru na mishi domin ni kaina ban gaji dajin dadin qamshinshi ba.yinin raran na murwu gun ya umar dan haka na gaji iya gajiya bayan bacci babu abin da nake sanyi.nan na matsa mashi ya maidani gidan su momy,muka shirya muka fito.na shiga gidan fuska daure ni a dole ban so na bishi ba.jamila tana xaune qofar momy tana yanka kubewa. Nafisa tanayi ma anty amrya kalaba, dukansu sai nagasun kalle ni sun kuma kalli junansu sun kwashe da dariya har anty na tsaya raina ya kara baci ina harara jamila sallamar ya umar sai sauka nutsu illa anty dake ta dariyart, shima wata 'yar dariya yayi tare da nuna ni da baki ina waigawa sai ya wayance sannan ya dake, na dubi jamilaa cike da masifa nace me kuka gani na dariya a jikina? jamila tace dole ne muyi miki dariya amma salon takusoyayyar tana birge mu, bakin ciki ne yasani saka kuka musammanganin yana su duka suka saka dariya da jamila ta gama mgn na shige daknmomy da kuka da sauri ta fito daga bedroom a rungumeni, lfy 'yar gidan momy sallama da kuka? cikin shesshekar kuka nace ba su ba suke mindarya, ta kamo hannuna zo inji waye kemiki dariya? sanda muka fito sai daryar sukeyi da lama mgn ta suke yi.momy tace dariyr me kuke mata kun sanillar dariya kuwa?jamila tace momy da. wasa mukemata fa,mu dariyr da mukeyi tace baa son yayanmu amma in yayi wayahar wani canza murya takeyi, dagazanje in amso sako shikenan shiru, sai yanxunzata shigo tana mana fushi? suka sake kwashewa da dariya, nace dukabin da kikeji zaki same shi jamila ai ga ya umar din nan ki tambayeshi in son shi nake ba dan ya matsa min ba wlh bazan bishiba har zakigaya min mgn momy. ta fara ma jamila fada, ya umar yace tokuina ruwanku ne? ance mukutana sona ne? yna mgn yanamurmushi sumasai guntse dariya sukeyi na [7:46PM, 17/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu 2----11 Ance mukutana sona ne? yna mgn yana murmushi sumasai guntse dariya sukeyi na kula ma sun maida ni wawaiya donhaka sai na wuce daki ina kuka momy ta shgo tana lallashina , gado na haye nata fushina har bacci ya kwashe ni ban sanlkcn dayaa tafi ba tun dani sai damagrib sannanmomy ta tasheni na farka naga turare a gefen amma dana sunsunabaya wancan kamshin dana sani,bayan isha'I na kira shi toilet na shige sbd su jamila 'yan sa ido nace mishi shi ne zaka ajemin wani turare ba wanda nace bako? yace to wanne kike so? na ce irin wabda kake sawa nace fa yace ai shi ne na aje miki nace bashi bane daka sanbaza kabani ba dabakamin alkawarin ba, na kashe wayr ya kira haba asmu bbu binda zaki nema gurna inki baki wlh wannan ne turaren danake sawaki yarda nace shi kenan yace kn yarda shine? nace eh sai anjima na kashe ina fadinbakasonbani kawai zakace shi ne. ina fitowa nafsa tacemanya, yanzun kuma wayar ma a boye akeyi? dama haushinsu nakeji gashi t kara tsokanata, nace duk abinda kike ji in jin shi nima zamuyi bala'I inbaku fita harkata ba, nafisa tace mu ma ki fitaharkarmu ki daina sa momy tana samu aiki tsaki naja Sannan na bangaje tana wuce, tayi dariya tace n son yayanmu ammaanki yarda sonshiake yi, cikin kwanakin ban da fushi bna komai, kafin daga baya na huce.wannan kron satinshi 3 snnan yazo, kila tun subahi ya fto don na farka dagabacci ne naganshi yace da yamma zaikoma,tare dani zai tafi tunda naji sauki nace ba zanje ba momy tace inyi hkr in bi shi sai zanzo hihuwa sannan gama bikin jamila nn da wata 3 ,haka nan na hkr na soma shiri su ko su jamila is tsiya sukemin wai dama momy ta daina bata bakinta dama sunji inacewa da zarn mijina yazo binshi zanyi, banza nayi musu sbd inji da takura min ma da batun tfy da ya umar yayi, munyi sallama dasu mama saurn dangi da nce banmusu sallamaba, saiya samin 2000 cikin waya wai na ma kowa sallama,abba ya shgo momy take gaya mishi zan bi mijina nan fa ya ringa wa ya umar kashedi a kula dani kada ya barni ba"a bani abin da nakeso ba, sbd abba kullum zai fita sai ya tambaye ni me nakeso? me zanci yazo min dshi? duk abin da nakeso sai naci shi ya hau minute ki. turaren ya umar shi ne kawai matsala ta yanzun son shi nake ammana rasa yaumr yaki y bani. Ina jin nty tana yima ya umar gargadinkad ya matsa min, dominhakan za iya kawozubewar cikin,n tuna rhma tace min snd tayi bari dr yace sbd yawan kusantar ta da mijinta keyi ne ya kawo zubewar cikin, a raina yandabanason cikin nan dama zai zube da naji dadi sanda muka isa gidnbabu kowa, na bude kofata na shga da addu'a bayanna danyishare share da goge goge nayiwanka da alwala hakazamna yaci gaba da tfy a gidanyaumar ina zuwaskul. farida sune suka gama yanxun. harkar kasuwanci yana bunkasa harma tanason ya umar yabart ta rnga xuwa dubai saro kayashi kam yace ya yarda da ita yasan Allah ne mai tsarewa,amma yasn xatakula dakanta, sbd tsoron Allahnta, sannan zai kara matajari . zuwan farko tare da ahj jamlu sukaje, sida suk gamahlewarsu satun ta 3 snnan yajibgo matakaya ta dawo kayanyaranajarira tajibgo waiya sya , jki na rawa ya biya tare da zuga mata albarka shi sarkin son yara. Bikin jamila ya matso lkcn cikina wata 6 ya fito ga cikin kato haushin ckinnakeji sbd hanani baccinda yake yi ga kafafuna duk sun kumbura kayan sun min kadan. bubuwan da ada nake son su yanzun duk bana sonsu. kamar su danwake, dudu madara da zuma da dai sauransu yanxun sai kamshin makiyana ya umar shi na fiso wta rigima ta ciki ashe turaren daya bani gashe shi neturaran a haka sai jikin shi d wannan damar shikuma yake samuna a cikin duk rana kun girkina, yjuy ni yanda ranshi ke so , ya kashe ni da soyayyarshi gefega kamshinshida nakeso fiye da komai. maltina bin shan ya umar ko yaushe yanxun nima tazamemin abin sha safe da rana. farida ko harkar kasuwancinta yasa bata cika zama a 9jaba wannan wta dama ceta hutawa da abokan harkarta. ya umar ya shgo ya sameni zaune turus a bakin gado yace a'a har yanxun baki shirybgashi harfarda ta dawo ta shiry.na dubi kayana cike da takaci sai hawaye na soma kuka, ya rude, lfy asmy ya taso ya tsugunn a gabana nace cikin kuka yanxun duba ka gani ji ba kayana kowanne yayi kadan da wane kay Wani kaya zanje kenan? ku tafi na fasa zuwa ya kunshe dariyar dakeson fitowa yasan inyayi ta ya tokano rigima,sabuwa yace kidansamu wani ki saka in yso da munje saiku shiga kasuwa da anty ki siyo zannuwa miki wasu, nace ni bazan iya zuwa kasuwa ba wannan cikin ne zai bar mutum zuwa kasuwa?yce to ni zanbar komai inje in kasuwar na saka jallabiya sai kayan kwalliya. ana saran kwana 2 zamu kadunan faridace a gaba ya umar ke jan motor ina jin su suna hirar cikin tana cewa ya ddace y bata duk babyn dana haifako? yace sosai ma ai danki ne ko 'yarki tace Allah yasa a haifamin 'ya mace mai kma da kai , mu gani wani suna ma zan sa mata? ta daga kai alamar tunani, can tace yauwa zansa mata ikram, inko na mijine insa mishi ikra'a, yace nafison fatima inko namiji ne muhd, haka suke ta zancen su inajin su, don tani dama zai cire cikin ya bata yanxun da nayi farin ciki burina ya sakeni, muna isowa da kyar na fito daga motar dama idan na zauna na dade haka kafata ke kumbura,kuma tashisai da dabara, da tamakon ya umar na fito daga mota muka shiga kowa sai sannu yake min. A tsakar daki na zauna na mike rashe rashe. mun gama cin abinci na watsa ruwa sannan nayi sallar azahar da la'asar. su shem'u da hadiza su rahma suka shigo kowa sanye da ankon lunching nace ina nawa ko baku dinka min ba? rahma tace mun isa maman 2,wane mu,na bata rai nace kada kimin mugunfata rahma biyun lfy? jamia ta shigo tace yawwa antyna ga kayanki da fatan kinzo da direbanki muna son yin amfani da motarki nace ya umar ya kawo mu fa. banzo da direba ba, na tash insaka kaya amma kaya sunki shigata da kyar siket dinya shiga amma riga taki bansan sanda na saka kuka ba sbd takaici na zauna bakin gado. su jamila da farko suna min dariya amma ganin abin nawa da gaske ne sai suka kra momy take ta saka gyalenta ta amshi kayan ta fita dasu takai ma teloli tana tsaye aka bude su ba laifi tunda sun shiga amma sun matse ni haka nan dai na daure daga gurin lunchingnace ya usman dayaje daukar rahma yakaini gidnmu gwamna road, sbd gadajan nan na su momy dana su mama dam yake da baki banyi mamakin ganin gida ta ciki a bude ba sbd Sbd nasan ya umar yana gidan, na hau sama duk daba son ya umar nake ba,naji zafin yanda na same su cikn gidan da ya umar kekira nawa shi da faridarshi suna minsoyayya cikin falosun shagala da shafar juna dogon tsaki danaja ne yasa suka dube ni na shige dak na ina zama bakingado ya shigo meyasa bakice min zaki zonan in zo in dauko ki ba? na dube shi gefen ido danme zance kazo ka dauke ni kana tare da matarka? na ci gaba, ba zaka tuna dani ba irin wannan lkcn ban damu daka tuna dani kokada ka tuna dani ba domin ba kai ne a gabanaba, burina in rabu da wannan kaddararran cikin inhuta. ya zauna kusa dani ko dai kina kisihina ne? nayi murmushin takaici kishin w? na nunashi kishinka? na juya na kwanta tare da fadin abinda kakeso shi zakayi kishi ni ka sani ban sonka da safe ban sonka, da rana haka da dddare baxan soka bane. ka sanini da kai ba zamuso juna ba domin tun farko in harakace ki ba zai taba zama so ba kaje kayi nazari ya kara matsowa kusa dani tare da tursasa murya kinyi kuskure asmy so yna zamaki tamkar yanda ki ke rikidewa ya zama so, na gani akan kaina domin ada naki ki asma'u amma a yanzun ya matso da bakinshi cikin kunnena,you are the one I love, Allah shine shaida ta yanzun ne nasan meneneso, koda baso nayi ba,ya mike zaki yarda nan gaba ya fita. farida ta koma mazauninta cikin sauri daga leken da takeyi taso taji menene ya umar ya gaya ma asma'u cikin kunne? Akwati guda haka ya umar ya ciko min da atamfofi,shaddoji da material suka kaima tela daga buba sai play da xani aka min sauran anko din ma duk manyan dinki akai min. ya umar xasu tafi da faridanshi washe garin daurin aure, dama yace ni inyi sati 2. ya kira momy falan abba sannan ya kira ni cikin waya, na same su yace ma momy kingan ta nan ta qi muje asibiti su yi mata awo dana mata magana sai ta saka min kuka, ga kumburin da take yi,na rasa yanda xanyi da ita gata nan xan barta sai ki kaita asibiti,ya ciro rafar yan dari biyar guda biyu gashi nan duk yanda akayh momy kin min waya, momy ta dauki kudin sannan tace shi kenan Allah ya kiyaye hanya ina faridar? yace tana dakin anty,momy ta fita nima na miqe xan fita ya kamo ni ya saka a jikinshi yace haba asmy ki bari muyi sallama da bebyna mana. nace daka sani tun kafin inxo kd ka gayamin cewa in mun xo xanga doctor mana,ka sani inhar ka gaya min baxan xoba, ka dinga tunawa sharadinka babu tursarawa, yace haka ne husna amma dan lfyrki da beby xaki asibiti Ke matsalarki daya ce baki san allura,tuncan abuja nace baxan bari a miki allura ba kinqi yarda dani na cire jikina daga nashi nace har abada baxan yarda da kai ba, ka tuna har qofar gidanmu ka dauke ni da sunan xan gwada takalmi ka kaini asibiti suka caka min allura da nufin xa amin gwajin HIV,ni xa ama gwajin HIV ka cuce ni, jikin ya umar yayi sanyi ya durqusa gabana gwiwa 2 yace ba kya yfy ne asma'u? ki xama daga cikin masu yfy ga yan uwansu a yayin da aka bata musu na sani na cuce ki ni mijinki ne amma kalleni gwiwa 2 aqasa ki yafe min ina so ki sani inna tuna abubuwan dana miki ina jin haushin kaina nasan laifukan dana makh ne ya hana ki sona, na kuma shaida ki na da haquri. na dube shi ya ban tausayi amma na dake na ce xan yafe makd ya umar amma sai randa ka sake ni na fita na barshi a gun.tsakar dare ya umar ya kasa runtsawa yanda ya tsani ciwo haka ya tsani asma-u ta furta kalmar saki, kana ya tsani ya xauna da laifin wani kanshi domin bai san ranar mutuwanra ba, Sakin asma'u baya cikin tsarin shi wayo kurum yake mata saidai yanxun yana ganin dole ne ya sake ta ko dan ta yafe mishi laifukanshi, wata xuciyar tace yaya xaka yi da santa? ya miqe yana xaga dakin ya dubi farida dake ta faman shirga bacci, ya sani yana san farida so na yarda da ganin girma da kuma mutunci amma san asma'u daban ne a hankali ya shige shi kuma har yau yana shigarshi kadan ya rage ya gama xagaye dukkan jikin shi ya xauna bakin gado tare da furxar da xaxxafan huci,sai yace menene maganin xuciyarshi can sai tabi amsa da cewa Allah,da sauri ya miqe tare da dauro alwala nan ya duqufa neman mafita gun Allah.Diamand hospital muka je da momy sunmin awo tare da dubani sunce baby lfy amma jininta ne ya dan hau, wannan kuwa ba wata matsala ce mai xafi ba yawancin masu ciki kan sama haka inka haihu sai ya tafi sun min allura,kuma sunce 3 xa-a min kudin in haihu inna haihu kuma amin 2 dama wai 5ce.ya umar ya saka ma ranshi dani,shine xaisa ya iya haqura dani dan gaka ya yanke shawaran barina kd.... [7:49PM, 17/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu 2----12 Yawancin masu ciki kan samu hk in aka harfu sai yatafi sunmin allura da dabara sun ce uku za ai min kafin inhaifu in na haihu kuma aimin 2 dama 5 ce ya umar ya saka ma ranshi wani sonta dani shine zai sa ya iya hakura dani don hk ya yanke shawarar baring kd inyi goyon ciki bayan na haihu sai ya sawwake min gidansu momy na cigaba da zama kafin cikin ya cika wata 9 kowa tausayamin yakeyi satin yaumar 4 sannan yazo yaci fada gun momy ya ce kiyi hkr tana raina yrny nan bana samun zamane shi yasa hkln shi ya tashi da ganin yanda na kumbura ciki yayi kato kowa cewa yake bai taba ganin ciki maigirma irin wannan ba sukan likitoci sunka hoto sun ce lfy ta lau hk ma cikina kuma watan cikin 8 bai isa haihuwa ba ya umar yaza kullum yana hanyar kd da abj dr ya ce indinga zaga gari hkn yakan tasani gaba mufita zagaye duk inda muka muce sai anmin sannu inko ina zaune ne hk zaita matsamin kafafu su dan saki yanaga min kalamai masu sanyaya rai inshallahu zaki haihu lfy kada ki damu kinji? Duk addu'a muke miki cikin sallolinmu kema kina yi? Me zaki ci? Hk zaita lallabina wani sa'in har tausayi ya ke bani. Cikin bacci naji kaman an tsungule na farka da kyar na sauko daka kangado ba nason nayi motsi mai karfi momy ta tashi bata samun bacci sosai bayan gida naji inaji don hk na shiga toilet amma yaki fitowa dg nan basai ciwo ya matsamin ba na fito na kafa kai jikin gado momy ta farka da sauri ta ce yayane asma'u ? Na ce bayana marata zan mutu momy ta ce kiyi salati da addu'a bari inyi waya usman yazo ko aliyu atare suka iso aliyu ya dauke mu nida momy usman kuma yaja su abba da anty dr na dubani ya ce haihuwa da saura yanzu ma nasoma nakuda domin ban bude ba jin hk yasa nasadakar mutuwa zanyi ban taba jin irin wannan ciwo ba don hk na sama raina tawa ta kare Shi kam yaumar tun dare jikinshi ya bashi kd babu lfy sbd mafarkai barkatai da yayi aranar tun asubahi yake kiran wayata amma shuru babu wanda ya dauka hankalin shi yatashi sosai yasan da tana kusa zata dauki wayar ko da masifa zatai mishi yakasa natsuwa sai kusan A zaton shi ni ce ya ce Asmy jamila ta ce ba ita bace ya ce tana ina? Ta ce em tana bayi don ance kada su gaya mishi ya dan ji sanyi har ya shirya fita kafin yakai ofis dinsu ya koma kira ta dauka ta ce bata kusa cikin tsawa ya ce ina taje? Nan ta dabure tarasa me zata ce can ta ce bari na nemota takashe wayar ya dubi direba ya ce yi paking a gefe nan ya nemi momy akashe ya nemi abba tana ringing ba'a dauka ba ya kira antynshi akashe duk lkcn su kam wayoyin su suma gida nan fa hkln shi yatashi zuciyar shi tagaya mishi asma'unshi tarasu nan take ya ce da direba sukama hanyar kd sun iso 11 gidan bakowa sai nafisa ya ce ina momy ? Ta ce na asibitin diamond ya ce shine don iskanci kika cemin asma'u tana bayi? Yana magana ne yana fita don hk bai ji amsa datake bashi ba sanda ya iso asibitin na jigata ba kowa guna sai likitoci yaumar ko gaisuwa baiyi da su momy ba ya ce musu ina nake? Suka nuna mashi dakin haihuwa sai ya shige dr ya ce yanlabe kayi hkr kajiramu waje ya ce madam nima kimin hkr naga matata ya nufo ni ya rungume ni sannu ya ke min tamkar shi nakudar take jira ta tashi gadan gadan amma haihuwa shuru likitoci sun ce dayan rana zan haihu amma har 2 shiru yaumar hkln shi yakai karshan tashi ya ce sumin aiki su cire adan in huta sun ce in ankai 4 ban haihu ba zasuyi min aiki ya fita don yo salla tunda sauran karfina har nakai bana iya koda nishi biyar dai dai anmin shirin aiki yan uwa sai addu'a wasu na kuka kada ma momy taji, A dakin tiyata wani sabon ciwo ya tashi wani uban nishi nayi sai ga yaro ya fito fit jim kadan sai ga sabon ciwo nan suka gane yan biyu ne suka taimakamin aka fito da ita nan suka fito da yaran don gyara dangi suyi matukar farin ciki da sauka lfy anshiya yara anata murnar ganinsu shi kam ya umar ni yake son gani dr ta ce kada yadamu ana kimtsa nine sun min allura sannan suka kaini dakin hutu bacci nake bansan irin hidimar da nake su ba sanda na farka tara tayi momy ce da ya umar ya taso da sauri sannu asmy kin tashi? Kallon shinake kurum a raina na ce badole kai min sannu ba tunda ka hada ni da aiki sai kuma naji dadi dana tuna yau ko gobe zamu rabu da shi ya ce momy a hada mata tea bari ta wanke bakinta shi yatadani na wanke bakina cikin wani kwanon silba sannan na dan sha tea kadan momy ta ce yarta baki ce ina abinda kika haifa ba? Shuru na mata araina ko fadi nake ina ruwana da abinda na haifa ya umar yaje gadon su yadauko daya ya ce kinga arzikin da Allah ya bamu asmy na kwanta naki kallon su da momy ta matsamin sai na ce ni ina ruwana dasu Shuru yayi yana kallona momy ta ce wanna karon zamuyi rigima dake asma'u suka fita fatima na ce yaya babu wani lallash ka bude mata wuta ba'a bada nono ke aka baki? Suka fita yazo gaban gado na ya zauna bakin gadon zcy shi tana har bawa yanzu ma bai san ta inda zai soma ba can ya tashi yaje ya dauko maccan ya zauna kusa dani ya ce asma'u ki hkr nasani duk komai laifina ne kada kiyima yaranki horo da laifin babansu ki bada nonon nan domin Allah ba don ni ba kinga ita macce tanada rauni na dube kasan baka mukayi dakaiba don hk bazan bada nona na ba yanzu ina takarda ta? Yayi ajiyar zcy kinsan zan baki tunda nina ce zan baki amma yanzu kisan zuyi ta jin haushin yan uwanmu zasu tsaneki na soma hawaye wannan karon na shirya na yarda in fuskanci ko wace irin matsala ce kai dai ka sallame ni yamike yana jijjiga yarinya sbd kukan da take yi yasa mata lebanshi abaki ya dan jijjigata sai tasoma bacci ya mannata akirjinshi sannan ya zauna bai san me zai ce mata ba yaje ya kwantar da ita sannan ya fita gurin dr yaje ya bashi bayani kan babies suna jin yunwa mamansu tana fushi ta hanasu nono dry likita yayi sannan ya rubuta kalar madaran da ta dace dasu ya ce koda tana basu nono ba dole ne ya ishe su ba dama sai an hada da madara yaje ya sayo ya kawo nan da nan aka dama masu suka soma sha shi kuma ya koma abj sbd bai sanar ba gashi suna cikin wasu bincike ne washe gari yayi lagos Nikam har sannan naki bada nono na, kwananmu uku aka sallame ni mukayi gidansu momy dama su abba basu sani ba haka nan momy ta hana a fada ma mama. Ran kwana hudu ya iso da kaya niki niki mota guda tamkar masu kayan tashi, duk na yara ne. Su rahama suka fita da su hadiza kowa baya jin dadi yanda yake ganina rai cunkus, bana cin abinci. Hadiza tace Allah yau sai na gaya wa mama, su anty aina'u. ma da gangan suka yi shiru har alhaji ma sai yaji. Rahma tace a'a ya umar ne yace likitocin sun ce kada a matsa mata fa! Hadiza tace ba dai ya son ya matsa mata amma na taba ganin mai jego ba cin abinci kuma ba zata ba yara nono ba sai shegen bakin rai? Ni kam dama na kosa su fita tunda naji zuwan ya umar yau kama sai ya sallame ni, ya zauna bayan ya dauko yarinyar. Bansan me yasa yafi daukar yarinyar ba, maman 'yan biyu na same ki lafiya? Banza nayi mishi yace yarinyar nan tana kama dake sosai, shi ya sa nafi sonta. Na harare shi, wannan ba damuwa ta bace ni yanzu damuwata ka sake ni, ban ma kaina adalci ba in har naci gaba da zama da kai. Duk sanda na dube ka ina tuna wuyar da ka bani tare da bakaken maganganun da kasha gayamin amma in ka sake ni zan yafe maka kuma raina ya huce. Ya tsugunnan gabana yanzun to wa zai shayar min da yarana? Wai zai kula min dasu? Nayi murmushi sannan nace ka manta da faridarka? Wacce ta iya yiwa yara tarbiya kuma 'yar masu tarbiya? Ya zauna kasa, ban da magana a yau amma kiyi hakuri. Nace na daina yarda kana min wayo da yawa, gashi ka samu yaran da kake muradi, san...sallamar mama ce ta katse ni, ina take mara hankalin yarinyar, dan ubanki ba a bada nono ni na baki nawa? Ta shigo bata 'yar ta bata nono ko in tsine mata yanzun nan. Ko kuma ki biyani nawa. Don kin sha wuya su suka dora miki? Ba Allah ne ya doro miki ba? Gani nan tun daga haihuwarki na samu hawan jini amma ban hana ki nono ba sai ke? Kuka na saka su momy suna ta ba mama hakuri tace ba fa zata tafi ba sai na basu nono. Ta dubi ya umar tace kai kuma faruk baka gaggaura mata mari? Yarinya mara jin magana. Ya umar yasa ta cinyata, momy ta ciro nonon ina kuka aka sa mata. Nan ko ta kama sai sha tace, shima yana bacci ya umar don mugunta sai da ya taso shi shima suka saka mishi nono ya hau sha, ranar nayi kuka har da ciwon kai. Da dare ya umar ya shigo na dan dube shi wallahi duk ya rame. Ya ce me da me kike so game da suna gobe zan koma jibi zamu zo da my farida saboda tana dubai yau zata dawo, na dube shi ina ruwana da suna? Ni fa babban sunana ka sallame ni. Yace zan sallame ki amma ki bari ayi suna mana! Nace ran suna? Yace da dare ba. Nace shi kenan yace to ki saki ranki ki dinga cin abinci kina basu nono, na ce nifa ba zan iya ba da nonon nan ba. Ya ce ke da su daya ne a raina kinji asmy? Yanda yayi maganar cikin muryar tausayi don haka sai ya bani tausayi. Ya umar ya kashe kudi da sunan nan tamkar a kasa yake hako su. Ni kallonshi ma nake yi. Akwati saiti daya yayi min guda biyar, zannuwa talatin da shida ga key din mota ta academy 'yar mai kyau sabon sanfur ga hajji da umara sannan ga takardun gidan shi na nan kaduna, yace na wane halak malak ko bayan ranshi ko ba ma tare nawa ne. Alhaji da mama fada suka kama yi wai duk iskancin da nake yi har ya birge shi ya min kyauta haka? Abba da momy cewa suka yi babu ruwanku wannan tsakanin miji da mata ne. Haka yasa ni jin tausayin ya umar nasan yana yi ne don in zauna dashi in daina maganar saki to ni bana son shi haka nan bana son 'ya'yanshi. Farida ma tayi hidina sosai, dangi sunyi hidima da mu. Akayi suna yara suka ci momu da abba, kowa ya wadatu da kayan suna. Rago biyu shanu bibbiyu haka ya umar ya yanka. Daren ranar na jira shi dan ganin takarda bai zo ba har sai da nayi bacci. Ya shigo yaran yaje ya tsuguna gabansu yayi musu adduo'I sannan ya sunbace su, yazo kusa dani ya sunbaci kumatuna sanna ya aje min wata 'yar farar takarda kusa dani, sammako yayi don haka bamu hadu ba, ni kam ban ma ga takardar ba sai da ina karyawa naga takarda na dauka da sauri ina dubawa. Cewa yayi: “ki min afuwa ba zan iya sakin ki ba saboda son da nake miki, ki zabi wani horo mai tsanani wanda kike ganin yafi kowanne horo wahala ki min shi, na yarda in dai zaki janye batun saki. Sannan ki taimaka ki kula mini da yarana domin ki tuna ko ba aure na san zaki iya kula min da yarana don zumunci. Kina da hakuri, ki kara hakurin na gode”. Tsaki naja sannan na yaga takardar, nace ba zan iya zama da kai ba in ko ka ki wallahi zaka ga wulakanci ganin idonka. Haka mukayi ta yin wankan jegon nan yara kam ko kallonsu bana yi, nono kuma sai momy ta tsaya a kaina sannan zan basu, in ko ba ta nan in dage ince sun sha. Satinmu uku ya umar yazo dubamu sanda shigo suna ta kuka ni ko ina kallon filn dina, kuma ina jinsu dama ko suna kuka sai dai wani ya dauke su ya basu ruwa, har mamakin su momy keyi wai ko da labari basu taba jin labarin shashashar uwa uwa irina ba, kashe TV yayi sannan yayi bedroom, ya dauko su yana duba na ranshi bace. Ban san irin qin da kike min ba asma'u, ko baki sona ai kya so 'ya'yanki. Na dube shi in dai ba zaka sake ni ba toh baka soma ganin takaici ba ya umar. Yayi shiru can yace toh bata nono shi kuma sai in bashi madara, nace bani dashi. Na mika na fita. Innalillahi wa inna ilaihir raji'un kurum yake ambata a zuciyarshi. Haka ya basu ruwa da madara, gashi ba aikin shi bane duk ya bata jikinshi. Sai ga nafisa ta dawo daga makaranta, nan ta taimaka mishi ni kam ina tsakar gida. Haka muka yi arba'in ko yawon arba'in bamuyi ba su abba suka ce maza in shirya zasu kira mijina a waya mu tarkata mu koma tunda iskancin da nake ma yaran kenan. Inje in ma zan kashe su ne in kashe su. Da na sa ma momy kuka sai tace kada in mata kuka itama tafi son yaran a kaina don haka bazata iya kallon cin fuskar da nake yi ma yaran kuma jikokin da tafi so duk cikin jikokinta, haka na hakura saboda dama gurinta kadai nake ganin fuska yanzu kan yaran nan har rahma tsiya mukeyi da ita. Waya abba yayi ma ya umar kan cewa yazo ya kwashe mu yace toh amma ba cikin wannan satin ba, saboda farida bata da lafiya yanzu ma asibiti zaije kaita. Abba yace assha, me ya same ta? Yace wallahi ciwon ciki haka ta kwana abba yace Allah ya sawake mata. Farida tana ta murkususu tamkar zata mutu, likitoci suna ta bincike kanta, ya umar tare da wasu abokanshi suna ta kai kawo a kofar da aka rubuta emergency. Kusan awa daya likitocin suka yi ta fita daya bayan daya, duk wanda ya umar ya tunkara sai yace yana zuwa. Daga karshe babban likitan ya fito ya dubi sy ya umar yace wanene mijinta? Cikin fargaba ko ta mutu ne ya umar yace nine. Likitan yace biyo ni office. Bayan likitan mai suna dacta bashir M ya bashi hannu sun gaisa yace matsalar matarka nake son shaida maka. Ya umar ya gyara zama. Dacto ya bar rubutun da yake yi yasa gindin biron akan habarshi. Kasan matarka tana shan giya? Ya umar ya mike da sauri, dr kace me ne? Kasan me kake fada kuwa? Dr yace calm down my friend. Da yawa matanmu suna irin wadannan dabiun. Ya umar ya katse shi to ni matata bata shan komai sai da coke ina zaton baka san aikinka ba. Ya fita yana masifa ya isko su aminu in da ya bar su. Yace kunji wannan wawan likitan wai farida tana shan giya, kuzo ku taimaka min in canza mata wani asibiti. Likitan yayi kokarin fahimtar da ya umar amma abin ya faskara dan yayi fushi sosai. Aminu da sali kam basu ji wani mamaki ba, domin sun jima suna zargin farida dan dai basu da shaida ne, amma sun taba ganinta da wani alhaji a wani guest house amma sai ta nuna musu wai matar mutumin ce kawarat kuma tare suke da ita ta shiga ciki ne. Su kuma sun san wannan mutumin mane min mata ne. Alhaji jamilu kenan. [7:51PM, 17/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu 2----13 Special hospital suka kai ta, a can ma sun ce suna zaton tana shan giya. Yace shi fa sam matarshi bata shan ko maltina sai dai coke. Sunce ko ma dai menene take sha to ta daina don ya soma lalata mata huhu da hanta. Sun cigaba da kula da ita bayan yayi waya mamanta tazo daga yola tana kula da ita. Suna nan su momy mota daya sukayi sukaje dubata har tana cewa ina yaranta? A ranar ne momy sukayi maganar dawowarmu ni da yara. Ya umar yace don Allah momy ta samo wata dattijuwa wadda zata dinga kula mishi da yara saboda ni makaranta. Momy tace ko ba makaranta asma'u bata son yaran nan ya ce tana son su momy kunya take ji. Kallonshi kawai momy tayi sannan tayi murmushi domin yanzu baya son laifin asmau. Haka akayi momy hajjo ta samo mana daga gombe mace mai son yara da tsafta tun a kaduna ta soma kula dasu, iyakata in ta matsa min in basu nono sau daya a rana. Ina jin nauyin hajjo musamman da take ce min anty. Banaso amma tace sunan babbar yayarsu gare ni don haka ba zata iya kiran sunana ba. Satin farida biyu aka sallame ta. Yazo ranar sati zai kwana mu wuce sundau, niko in da nake ma bai nema ba ya kwashi yaranshi masu hakuri inji momy tare da nafisa suka fita. Tun dare na soma shirin kayana kamar yanda momy tace inyi. Ban sallami kowa ba saboda na kula kowa haushina yake ji gidan mu kawai na shiga mukayi sallama. Mama tace dama ina so in gaya miki yarannan amana ce Allah ya baki kuma ranar gobe kiyama zai tambaye ki yanda kika bi dasu. Don haka kije ke da Allah in kin cuce su. A mota ya umar yamu da hajjo dasu sayyid da sayyida shine sunan da muke kiran yaran su anty aina'u ne suka samusu sbd sunan momy da abba ne nima zanshiga baya hajjo ta ce keko anty me zai kawo ki nan ga mijinki gaba? Ya ce a to gaya mata dai hajjo. Na koma gaba nazauna banida walwala har muka kai abj dakina na farko nan naga amaida dakin hajjo wani daki na kusa dana shi wai shine nawa kenan nida farida mun sakashi tsakiya lallai yana nufin zama zanyi Da dare ya shigo muna zaune da hajjo tana cin abinci ya ce intagama inje in nuna mata dakinta nima nakosa mu kebe sbd ina son takardata ko ta halin yaya ne. Na kai ta ta ce don Allah ki lura da yaran sbd dare koda zasu tashi kibasu ruwa na ce bamai hanani bacci na gwarama ki kauso su nan ta ce to andebo su mun samu yau mar yana gyara musu kwanciya hajjo ta ce dama nazone in tafi tasu ya ce barsu nan hajjo nan zasu na kwana insuyi wayo sai sukoma hannun ki ta ce to sai da safen ku tafita nashiga na zauna kan kujerar madubi ya dube ni kin watsa ruwa? Na ce ance maka nayi datti ne? Ya ce a'a na ce ba damuwar ka bane yanzu yaya maganar mu ? Ya ce aike kin cika hanzarine ina son insake ki akwai abubuwan da nake dubawa ne shiyasa kinga yanzu matsalar ki yarannan sbd su kowa haushin ki ya ke ji hakan bayamin dadi don hk nake son ki daure kishayar dasu na shekara daya sai in sallame ki hkl kwance yanzu amshi wannan ya mika mani wani dogon file wannan ki adana na yaranki ne kowannansu yanada hannun jari tare da acct din su na bude musu don care dubu dari bibbiyu nace ai kabar su gurinka ko kuma kaba farida tunda dama ita zaka basu ya ce ke nace ki adana na ce bazan amsa ba zanyi magana ya pls na amsa shi kuma ya fita wai yana zuwa gama shirin bacci na saka rigar bacci na kwanta na ba yara baya ina addu'a ya shigo ina shafawa ya zauna kusa dani shi shirin bacci yayo gajeren wando da rigar bacci mai budadden gaba na dubi kirjinshi gashine kirjin yana sa jin wani yanayi don hk na kauda kaina ya ce sufa bakiyi musa addu'a ba ban tanka shi ba nayi kwanciyata yayi musu addu'a ya kwanta bayana jikinshi ya jawoni na ce menene wannan hk? Kasan dai yanzu babu wannan a tsakanin mu ko? Ya ce dama ai shekara 2 na ce yasoma shafata to yau kadai kimin taimako na matsune na ce ka matsu da me wai baga matarka nan ba? Ya ce ai itama babu lfy na ce gaskiya ni yamanna bakinshi cikin nawa na soma mutsu mutsu amma tuni yasan hanyoyi janye hkln diya macce tuni na manta da batun ki maka lulu duniyar ma'aurata sai da komai ya natsu sannan naso jin haushin kaina na tashi na shiga wanka shima hk yana yana fitowa ya haukan sallaya yashiga kaim ubanjigi kukan shi ina bacci cikin dare sayyid ya tashi kuka ya saka babanshi ya dauko shi kusa dani ya zauna ahkl ya ciro nono ya mika mashi cikin bacci naji ana shamina nono na tashi da sauri yasoma shafamin kai yi hkr kinji kadan zai sha na ce shine har da sata? Yayi dry basata ba srry pls Muna zaune cikin sabon dakin nawa hajjo tana ba sayyid madara ya umar ya shigo cike da murna ya ce sannu hajjo suna shan madara sosai ta ce suna sha ai yaran nada hkr ya ce sun gado mamansu ne ya dan dube ni itama uwar tasu akwai hkr na kau da kai gefe ya ce kuzo ku gaida farida sbd ta kwanta asibiti hajjo ta ce to ta dube ni taso muje anty natashi muka shiga dakinta tana kwance tana waya ganinmu yasa ta dauko dogon lbr na ce da hajjo zomuje ta ce a'a bari tagama hk na hkr sai da tagama mun gaisheta ta amsa cike da isa ta dubi sayyida dake hannun hajjo ta ce wakike da suna ? Zo nan hajjo ta mika mata tare dafadin ga sayyida nan ni dai nafita na barsu ciki Kai ya umar akwai shegen wayo, haka yake min wayo shi ya same ni sannan su sha nono. Da rana ne ma ba na basu, yace ma hajjo ko basu sha da rana ba kada ta damu, suna sha da dare. Ko ran da baya dakina sai sun sha yake zuwa ya kwanta. In ko yayi tafiya ne bana basu, komai ma bana musu. Hajjo ce wankansu, wankinsu, cinsu da shan ruwansu. Farida kan dauke su amma da ta samu sauki fa ba sauran zama sai yawo. Yau ma da take zaune cikin supermarket dinta kallon matashin yaron takeyi wanda yake cikin yaran da ke kula da gurin ta, jin sha'awar yaron ya shiga ranta sosai, don yau kam za ta neme shine. Sssss ta mishi alamun kiran 'yan gayu, ya juyo ta kira shi da hannu. Yazo cikin girmamawa ya dan rusuna tace ka iya jan mota? Yace na iya madam. Tace to zaka kai ni gidan kawata. Yace toh. Suka fita bayan ta ma mai kula da yaran bayani cikin mota take tambayar shi shi dan ina ne? Yace shi dan taraba ne. Tayi ta nuna mishi hanya har suka isa maitama gidan su aminiyarta lady. Ta shiga suna ta lido ita da saurayinta, ta kira lady gefe wani yaro ne da na jima ina jin shi a raina, so nake inji irin nashi kwazon. Lady ta saka dariya yaushe kika tashi ciwo, amma kin koma jarabarki. Toh kin gaya mishi? Tace a'a, lady tace toh ni dai zamu bar muku gidan. Ta shigo da yaron, ba ta bata lokaci ba gurin nuna mishi nufinta, saurayin mai tashen balaga sai wanda Allah Ya tsare. Take ya yarda da nufinta kuma ta yaba ba laifi, sai dai bai kai mijinta ba. Haka tace a cikin ranta. Allah ka tsare mu da sharrin zuciya. Cikin haka muka samu 'yan watanni kamar hudu, yara sunyi kwari gwanin sha'awa inji mutane. Suna zama kowa ya gansu sai ya kara dubansu. Tuni na cigaba da karatuna. Ya umar yace ya kusan soma hutunshi in shirya zai dinga koya min mota. Nayi murna don ina sha'awar tuka mota sai dai ban nuna mishi ba. Tafiya ta same shi ta gaggawa kuma sati uku zasuyi a can kara benin. Don haka yana ta bar mana amanar yara, nace kai ma kasan ban da lokacin yaranka. Ya bar su ga farida da hajjo sannan ashe ya hada computer shi yana son ta ringa dauko mishi yaranshi kafin ya dawo. Bayan tafiyarshi na lura da wani abu, farida tana son yaran ne na ganin idon babansu. Tunda ya tafi bata kula su. Ni ko bai dame ni ba. Ko hajjo ma ta kula, don haka ta min magana. Nace su suka sani, tace koda yake kema uwarsu kin ki su bare ita da ta gansu a sama taka? Allah ya shirye ki. Na taba ganin inda ake son uba amma ba a son yara? Na dube ta nifa bana son shi hajjo, tace tafi can 'yar nema, yarinta ko da nake tsohuwar da kike kina son mijinki. Naki salon son ne haka. Na dafa kirji. Allah hajjo ba sonshi nake yi ba. Tace ai sai kiyi. Na jima cikin daki ina mamaki, yaya kawai ta min fassara wai ina son shi, yaya ma son yake? Na taba son suraj amma bana jin zan tuna yadda so yake, me yasa hajjo tace ina son mijina? Naga bana mishi magana, ban mishi dariya amma tace ina son shi. Gidan aminu muka je yau ni da hajjo, tace zata bini don ta gaji da zaman gidan. Aisha matar salis nan muka same su tare da aminan aminu. Mun sha yini in da muka sha hira soasai, sai biyar muka bar wuse wato unguwar su amina. Mun dan shiga kasuwa sannan muka yo gida. A falo na ga dankwalin lace din farida. Na wuce shi, hajjo ma ta shigo dauke da 'yar daya a baya daya a kafada suka yi dakinta. Ina bude kofa na ga sun fito daga nata dakin ita da wani saurayi, da ganina sai duk suka rude. Ta soma mishi magana kace ma anty aminan zanzo kaji ko? Allah Ya kiyaye hanya. Cikin in ina yace ta za..za su ji. Ya fita da gudu gudu sauri sauri. Ta dube ni tace 'dan yata ne. Na taba baki ba tare da nace uffan ba, na shiga daki ina mamaki. Ba wani da zai zo ta kai shi bedroom in har gaskiya za a bi ko yaya suke. A raina nace biyu kenan, dama na taba jin hirarsu da kawayenta. Ya umar da ya dawo ya sha mamakin yaran nan. Sayyida har yi take tamkar ya tashi daga zaune ta kamo shi, sai daga mishi hannu suke yi. Niko na share su. Yau kam ko sannu da zuwa ban mishi ba, nace in shi yasa hajjo take cewa ina sonshi to na daina daga yau. Tsaraba kam yara sun sha ta, washe gari ya fara hutu. Nan ya shirya mana fita ban ma sani bani da hajjo da yara, tunaninshi daya farida. Amma ga mamakin shi da yace yana son ya kai yara check up turai sai ta nuna yardarta. Tare da fatan khairan. Nan ko itama dana tana da fita da alhaji jamilu. Tafiyar da take saka ran shakar kudi masu kauri, har million ashirin. Alhajin na sonta musamman yanda take yadda yayi luwadi da ita son ranshi. Auzubillah. Ce min kawai yayi shirya zamu je kd, munyi musu tsaraba na kura kowa yaji dadin ganin yara bul bul, can na samu labarin fita zamuyi a bakin antyn shi, ban nuna mata ban sani ba. Zaune nake a falo ina kallo su sayyida suna ta guje gujensu, sam dama ba sa zuwa gurina tunda ko kare gurin mai kula shi yake zuwa. Hajjo tana kicin tana tuwon masara, tace ta gaji da ciye ciyen nan, nace nima zanci. Ta mana kuka dama muna da su duk momy tana bamu. Farida ta shigo yara suka nufe ta da gudu, suka rike ta. Kinga wani ball da tayi dasu tayi ciki abinta, wani irin kuka mai cin rai suka saki sannan suka shide. Wani abu naji yazo ya tsaya min a raina, ina kallon su tare suka mike a gigice suna kallona suka nufi dakin hajjo. Na mike da sauri na bi su na kama su na rungume sai naji hawaye yana zubar min, na kwashe su zuwa dakina. Na lallashe su suka kwanta a cinyata sai ajiyar zuciya suke yi. Baccin wuya ya kwashe su na tsura musu ido cikin jin tausayinsu, nan ko sai naji wani son yarana yana ratsa ni. Jin motsin hajjo sai na zame jikina na kwantar dasu na tashi bakinsu duk ya kumbuta. Ai ko hajjo ban ba labari ba, don ni zata ma fada. Ranar dakina suka kwana, na rungume su yau ce rana ta farko da suka ji dumin jikin uwarsu. Da safe ni na musu wanka har hajjo tana min tsiya. Yau kuma ana yi da 'ya'yan nawa ne? Sai da ya umar ya shigo ya same ni ina gyara ma sayyida gashi na raba mata gida biyu, na kama mata da ribbon kalar rigarta da takalminta. Ranshi kar amma baiyi magana ba yana Tsoron in yayi magana zan fasa gyaran, yace babyn baba me ya same ku a baki? Nace sunyi karo ne. Yace iye! Sorry zo nan yarinya na kinyi kyau. Ta tafi tana murna tare da fadin dady sweet ata, na soma shirya sayyid shima kayan shi masu kalar ja da fari tamkar nata. Ya umar yaji dadi, don har kama su nayi suna gulmata shi da hajjo yana gaya ma hajjo don Allah kada ta min tsiyar abinda nayi ma yara kada ma daina dan yasan halina. Mun dawo da kwana uku muka tafi, england muka fara sauka. Dakin hajjo daban namu daban. Ya umar da mukayi cikin wannan kasa nakan manta wai ba son shi nake ba. Kananan kaya ya kai ni na jibgo abin son raina. Kullum ya sani in tsuke mu tafi shakatawa, a raina na kance ina malumtar? Guraren wasanni mu shiga motocin dake gudu kan kankara, mu hau dokin keke da dai sauran su. Ko ina ina manne dashi satinmu biyu mukayi america sannan mukayi dubai. Watanmu biyu na zubar da karatun da nake ikirarin so na kama bin miji yawo duk da ni ba haka nan na so ba. Muna dawowa na tada ballin saki, haka yayi ta lallabani yana cewa in bari yara su shekara. Cikin yardar Ubangjij watansu goma suka soma tafiya, nan fa nace na yaye su dama ba basu nonon kiriki nake yi ba. Ya umar yace to shi kenan. Na ta da tsiyar saki, yace dai a bari sai ranar lahafi. Dadi naji zan kuma nuna musu cewar ina son ya umar ba haka bane. Lahadi tana yi yace muje kaduna zai zo ya kawo min, sannan ya min godiya har da cewa aikin ma min kokari asmy, ni naja motar sabida a rayuwar mu ta england ya koya min mota, kuma ban sha wahala ba. Sai dai ban taba doguwar tafiya ba sai yau, yau ma don ya riga ya fita ne ni ko naki kiran direba. Cikin yardar Allah muka iso lafiya. Kwanan mu daya gurin su momy, ya aliyu yasa aka gyara mana gidanmu muka tafi can. Na zauan zaman jiran saki. Wata sabuwa! Ba sai ciwon kirji ya sarface ni ba? Baya, kirji abin babu arziki muka yi asibiti. Wani kayan takaici gwajin farko wai ina da ciki wata uku. Nace ciki? Wai ciki. Tun a asibiti na mishi waya nace sai kazo san yanda za ayi dan wallahi dacto yace ciki garan. Kazo sai dai a zubar...ya katse ni, kada ki zubar min da ciki, ki bar ni dai zanzo nace to gara kazo, na sha kuka tamkar wadda ta yi shege. Hajjo fada tayi ta min, washe gari yazo yace to gashi yazo yaya zamuyi? Ina kuka nace zubarwa ce zamuyi. Yace to daina kukan abi mai sauki, shirya muje. Ashe ya kira dr sun hada baki da muka je likitan ya dan dudduba sai cewa yai akwai hadari a cikin aikin wai zan iya mutuwa. Ya umar yace toh fa! Yanzun ya za'ayi kenan likita? Likitan yace mu bari sai nan da wata hudu, zai dai bani magani wanda zai sa abin dake cikin ya rasu, in yaso su sai su sa injin su markade shi. Ya tulo min kwayoyin magani ashe duk na karin jine ne ban sani ba. Naje gida nayi ta sha har da wuce ka'ida ni dole zan kashe abin dake cikina. Satinmu biyu yazo ya lallabani wai in dawo abuja kada su momy su kula ina da ciki su hana mu cirewa. Kai ya umar sai a bar shi. Tun daga sannan na kama 'ya'yana, nan na shiga yi musu hidima. Su kuma suka daina zuwa gurin farida koda tana zaune da babansu ne. Dan munafunci sai ta ringa cewa mamanku ta raba ni ku, shi kam sai yace sha'anin yaro ne yaya mamansu zata raba ki dasu? Sai tace toh ba gashi ba tunda ta ja su suka ki ni, nikam wata hudu yana cika na tada balli domin lokaci cikina wata bakwai naki zuwa kaduna don kada ma su ganni da ciki su min tsiya, nan ya shiga lallashina wai zamu canza wani asbiti. Muna cikin haka ranar sai ya shiga dakin shi don ganin shirmen yaranshi da na musu birthday baya nan. Ya tuna da na'urarshi mai dauko mishi komai kunne take. Tun daga can suna kanana ya soma kallon da shirmen kin da uwarsu ta musu ya kan sha dariya yanda take satar kallon yaran a lokutan baya da bata son su. Kwatsam sai dan duhu kan abin kallon can sai ga wani saurayi gabanshi ya fadi yace wanene wannan? Farida ta fito daga dakinta sanye da gajeren wando da kuma bireziya. Innalillahi yake ta maimaitawa, cinyar yaron ta zauna shi kuma soma shafa cibiyarta. Ba zai jure gani ba saboda jininshi da ya hau. Nan take ya kashe sannan ya zube a gado, sunayen Allah ya shiga jerowa sannan ya samu sassauci lokacin ne wayar shi ta soma ruri kamar kada ya daga sai kuma ya duba aminu ne yace in da hali fito mu hadu nan area 23 zamu gwada maka wani abu mai muhimmanci. Kamar kada ya fita, sai kuma yaje ya dauko mota. Gidan shakatwar alhaji jamilu suka shiga inda aka shiga da farida da zuwan kamar minti talatin. Salisa yana aiki da wani kamfanin ne mallakar alhj jamilu shiyasa ya san shi kuma alhj jamilun yana sanyo salis cikin lamuranshu saboda yanda yake da amana. Shi yasa ake da ikon shigowa gidan shakatawar dan wataran anan ake lissafin ko shawara. Kai tsaye falon suka shiga inda suka leka dakin barcin inda ya umar yaga faridarshi haihuwar uwarta ana luwadi da ita. Wa iyazu billah. Faduwa yayi su salis suka fita dashi. [7:54PM, 17/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu 2----14 Faduwa yayi su salis suka fita dashi sai da yasha ruwa laida biyu a ranar amma da yake jarumi ne sai ya dake. Wata tsana da gami da kyamar faridar suka shige shi. Tsoron daya ko suna da HIV tun kafin ya bar asibitin yasa aka mishi gwaji babu komai tare dashi, don haka yayi ma Allah godiya. Tara saura ya shiga gida amma bata dawo ba, falo ya zauna gidan ma babu wanda yasan ya dawo sai ni ce na fito dakin hajjo naga mutun zaune tamkar gunki. Na shige tunda dama ba wai ina shiga sabgarshi bane. Don ko shi ya sani sai naga dama nake tanka shi. Tara da kwata ta shigo cikin hijabinta na sutura, har kasa a ranshi yace FUSKA BIYU. Ta nufo shi da fara'a. Sorry sojana kana ta jirana inzo in baka abinci. Ya daure yayi murmushi kada ki damu na sani harkar kasuwanci ce to ya kasuwa? Tace alhamdulillahi mun gode Allah. Ta nufi daki barina rage hijabin nan. Ya ce to, ta fito cikin leshi ja hannunta dauke da gwangwanin coke dayan maltina. Kusa dashi ta zauna ta mika mishi maltina, kasha naka in sha nawa. Yace yau nima naki zan sha. Tace toh bari na dauko maka wani. Yace bani wannan ma ya ishe ni. Ta mike bazan baka ba tana dariya wai ita wasa. Ya gane giya ce ta zuba, yace yau naga abin ala'ajabi. Ta zauna, a ina? Kuma me ka gani kai da baka cika damuwa da lamuran mutane ba, yace to ai yau nasha mamaki. Wani soja ne cikin wannan barikin ya kama matarshi da wani, ta zauna da gaske kake fada? Yace sosai ma kuma matar aure kace? Yace Allah matar aure mijinta kuma salihi ne dan tare muke. Tace innalillahi, kai wannan tayi asara. Ita ko ina zata kai zunubi, kina matar aure sannan kina bin wani? Sojana anya mutane sun san girman zunubin zina kuwa? Balle matar aure ga hakkin miji ga na Mahalicci? Tir da wannan mata. Kallonta yake cike da mamaki bai san tsawon lokacin da ta dauka tana cutarshi ba. Yace kinsani my farida yanzun ji nake in ni ne wane mataki ya kamata na dauka a kanta? Kashe ta zanyi ko hukuma zan hada ta dasu? Tace ai ba zancen hukuma in yana son ya more mata ko ya sake ta dama kaga ai in haka ta faru ba aure. In ya sake ta sai ya barta da Allah ya isar mishi sannu kan hankali sai Allah ya saka mishi da mata ta gari. Ita kuma zata ga karshenta. Ya mike cike da murmushi, shawararmu tazo daya my farida. ya mika mata takardar sakinta uku, yace gashi kinga karshenki, sannan tuni Allah ya min sauyi. Kije Allah ya isa Allah ya isa ban taba zina ba, nagode Allah da bai bani haihuwa dake ba. Yayi daki ya bar ta nan cikin mamakin wannan lamari. Bansan hidimar da suke yi ba sai dai washegari naga ya shigo da wasu zaratan sojoji sun fita da kayan farida sai kangon dakin. Ga zatona sabon gida ya gina mata ta tare tun da naga itace matarsa. Sai dai ganin ko yaushe yana gida na soma zargin ko sun rabu ne? Wata kulawa yake mana wacce tafi ta baya. Kullum yana lallashina ni kam kara botsare masa nake. Yau dai da muna kwance yace ya min alkawari na karshe da zasuyi ya dawo zai sallame. Cikin satin tafiyan wata biyu zasuyi wata haihuwata zai dawo. Suka tafi dan kwantar da tarzoma tare da runduna karkashinsa. Ranar tafiyar tamkar kada ya rabu da 'ya'yansa. Nima ya rungume ni sannan ya durkusa gabana wai in yafe masa laifukan da yayi min wanda ya sani da kuma wanda bai sani ba. Cewarshi ko ba zai dawi ba, jikina yayi sanyi nace tunda kace in ka dawo zaka sake ni na yafe maka. Yace kina sona? Na girgiza kai alamar a'a. Ya fita sai wata zuciyar ta ce kilan tafiyar kenan. Sai kuma hankalina ya tashi. Kaduna muka koma kowa ya sha mamakin ganina da tsohon ciki ga yarana dake bibiyata ko ina na shiga. Yanzu nima gaban kowa nuna musu so nake balle ma da babansu yayi wannan tafiya sai naga tamkar sun zama marayu. Su rahma da jamila suna min tsiya kai matar nan da gulma take, bana son miji bana son miji sai shegen hadama, har kin kunso wani cikin. ban da ta cewa wai barawo hannun mata, kowa haka yayi ta min tsiyar nan ni damuwata ta dame ni tunanin mijina. Sai yanzun na yarda da batun su hajjo na cewa ina son mijina domin yanzu na kasa kuzari ko yaushe ina kwance da tsohon cikina ina tunanin mijina tare da tuno tafarkin rayuwarmu har zuwa yau. Waton yadda na dauki ya umar ba haka yake ba, ba mugu bane wancen karan yaki halina ne da yake zaton ina dashi. Ko zaman mu na kudu bai taba hanani ci da sha ba. Kuma yana horani ne in nayi masa laifi. Sannan bakaken maganganu da na aikata maganganu ba laifi bane dan ya gaya min su, tunda ya gane zaton shi ba haka bane fa? Yana kyautatamin, yana tausayamin kuma yana nuna yana sona. Ya umar yana da alheri, sadaka, kyauta, zumunci da kuma adalci. Na tuna sanda ya ba farida jari haka ya siyo min gold na daidai kudin da ya bata yace in ajiye. Na tuno irin soyayyar da yake min a lokutan da muka kadaita don auratayya. Nayi juyi na rungume pillow na saka dayan hannuna ina shafa cikina wanda muka same shi muna tsaka da soyewa a london. Ina son cikina, na tuno sanda ya umar zai bar gida yaso in fada mishi kalmar so na kasa, in bai dawo ba ba fa? Nan kuka ya kwace min cikin kukan nake fadin ina son ka ya umar don Allah ka dawo zan gaya maka kaji, ina tsananin sonka. Na fito daga wanka na koma ban shafa mai ba na saka kayana ban daura dankwali ba na xari hijabina .tunanina ya sha kaina tun gun wanka nake kuka,yau fiye da wata ya umar babu waya in na kira tashi sai ace min tana rufe, ni kam bai ta ba min irin wannan tfy ba,na fito falo hajja da su sayyada suna kallo catun.. Na xari key din mota,dama motocinshi duka ya xube min keys,ban da tawa, sayyida ta dube ni anty an biki,anty suke kirana dan sunji hajjo tana ce min, na kalle ta xo to muje, na dubi sayyid yaran akwai haquri nace xaka? ya daga kai alamar eh, nace to xo muje, hajjo tace anty ina xaku je? nace gun su momy tace to sai kun dawo, na riqe musu hannu muka fita sayyid yace anty banbino aje, nace a'a sayyid yace dady mun je ko?na kalle shi kana san ganin dady ne babana? ya ce um sayyida tace nima ,sabon hawaye ne ya xubo min ina yin parking a qofar su momy ya aliyu tsaye shi da wani suna magana.sayyid ya ce anty ga uncle suna sauka gunshi suka nufa ni kam ciki nayi da sauri. na tasa momy ina kuka tace me ya faru? hankalinta tashe,cikin kuka nake gaya mata halin da nake ciki tace min dama yacd mata inda xasu je daji nd inyi haquri in Allah ya yarda lfy xai dawo, aliyu ya shigo da yara nan suka yi ta lallashina har na haqura muka yini sannan muka koa gida. Yau watanshi 2 cur na xuba ido shiru har dare wasa wasa har sati duk na fita hayyacina ga ciki ina gani tsabar tension ne ya sani naqudan dole, naqudan ma ta jini, tunda EDD dina saura kwana 10, kwana na 3 a asibiti na haihu yaro namiji qato, sai dai na xubar da jini sai da aka min qarin jini, aliyu da usman suka bani, an sallame ni duk da ya bar komai hannun aliyu, cewa nayi baxanyi taron suna ba, abar ni inji da kaina, da kuma damuwata, suna kuwa da su abba suka tambaye ni nace susaka sunan ya umar nasan mun rabu kenan yanda nake yi suma duk na karya musu xuciya hankalinsu suka tashi, kai wasa wasa har muka yi arba'in su aminu ma suna xuwa suna kwantar min da hankali shine mai kawo min lbrn halin da suke ciki yace har an qara tura su wata rundunar sbd abin yaci tura, sai da qar ya kwantar min da hankali ya kance wai shi suna waya,inma musa sai hajjo tace kada kiyi musu anty kin san fa shima soja ne sai ta yuwu hakanne. Kwatsam rannan ya aliyu yaxo min da lbrn sun dawo suna abuja,amma an riqe su sbd xa ayi muru qarin girma.murnan dana ringa yi har mamaki tayi ta ba mutane. sai kuma ahanyan su ta xuwa lagos jirginsu yayi hatsari, mafi yawa sun mutu,ina xaune ina kallan lbrn CNN da misalin 12,sai ga lbrn da duminshi,wai jirgi mai dauke da man yan sojojin da xa'ayi ma qarin girma ne ya fadi,jirgin yata so ne daga lagos xuwa abuja,ai ban gama jin xance ba na saka ihu,ashe gida sunji ance kada a gaya min domin hajjo tana musu waya tace gani nan na fadi sume bata san me ya faru ba,nan momy ta saka kuka tace shi kenan wani ya gaya mata,farkawa nayi na ganni a gadon asibiti kuka nake sosai musamman dana ga daukachn yan uwana su momy ne ke lallashina ita da mama,mama tace asma-u ai shi bai rasu ba, nace ya mutu ba kwasan in sani ne,lkcn ma su kansu ba sani sukayi ba,jinina ance ya hau dan haka sukaimin alluran bacci na samu ya dauke ni xuwa yamma sunji bai mutu ba suna asibitin sojojh dake can abuja. Su abba sun dugunxuma can ina farkawa na samu lbr nafa ce saina je aka yi ta lallashina kan in naje hankalina xai tashi ne sbd ko su an hana su gani shi.da qar nayi sati tsabar kukana da rashin cin abinci yasa aka ce su barni inje.da qar suka barni na shiga gun shi.na sha kuka ganin yanda kusan duk jikinshi an nannade shi gidanmu na abuja muka dawo,cikin satin ya soma motsi na liqe a asibitin nike kuka dashi addu'oi jama'a sai yi suke masallata har da isalamiyu sbd ya umar mai jama'a ne ga alheri shi yasa kowa ya damu da ya fara jin sauqi, sai me? duk damuwa da kuma hidiman da nake yi dashi sam baya min walwala ko sakin fuska. da farko na ce ciwo ne amma da yaji sauqi fa? sai dake min tare da shan qamshi, watan shi daya aka sallame shi kuma cikin satin wanda suka yi saura suka samu qarin girma, harda ya umar a cikin wadamda suka samu prmt, kowa nata murna abokai sun shirya dinner mi kam tsoron shige mishi nake, shi kam yana yine sbd kada na mishi xancen saki. Bayan duk wadannan bidirin yau na fito wanka bayan sallar isha'I yara suna gurin hajjo har da junior. Kwalliya na zauna na soma tsarawa. Yau kam na dauki aniyar nuna ma ya umar ina sonshi. Zan gaya mishi baki da baki kuma zai gani a aikace. Sosai nayi gayu, dakinshi na shiga abin da ban tabayi ba shine zuwa turaka. Sanda na shiga yana sanye da gajeren wando fari sol haka singiletin jikinshi. Yana rubuta wata 'yar takarda. Ina shiga ya hada rai tamkar yaga mutuwarshi, yace yawwa gashi. Jikina ya soma bari nace me zan gani ya umar? Ya dubeni duban wulakanci abin da kika dade kina so ne na baki. Kasa na zube gwiwa biyu ka min rai yaya zaka yi da yarana? Yace ki amsa yaran da dama ba wai kina son su bane ko dama da kika wulakantasu me ya same su? Na rike mishi kafa kada kamin haka. Yanzu ina sonka ina kaunarka. Yace karya ne ke da kanki kin fada. Bakin da yace ki, ko yace so karya ne don haka amshi ni tuni na samu matar aure. Kingama hoton ta nan, ban kalli hoton ba na amshi takarda na fita ina kuka, na dauki gyalena tare da key din mota yana zaune falo nazo wucewa yace au na manta batun karatu in kina bukata zanfa taimaka. Cikin kuka nace banaso ka cuce ni ka koya min yadda zan soka a karshe ka tsunduma ni cikin kogin sanka sannan ka sake ni, ban yafe ba. Yace haka kika min. Na tafi na rasa inda zan nufa. [7:59PM, 17/10/2016] 🌹@lh@ji🌹 A R: Fuska Biyu 2----15 Karshe Gidansu naje a tsakar gida na saka ihu da gudu su momy suka fito dasu anty cikin kuka nake fadin ya umar ne ya sake ni. Saki? Inji momy. Shiru abba yayi, anty tace me ya hadaku? Nace ni ban mishi komai ba shine yace wai ba ya sona yanzun ya samu wata. Momy tace anya bai samu matsalar kwakwalwa ba hadarin nan? Abba yace ku shiga daki bari na neme shi a waya. Muna daki sai kuka nake ba ran ma da nonuwana suka soma zuba wannan alamace ta junior ya tashi, nace momy dan Allah ku bashi hakuri ban san me nayi mishi ba yaace ya sake ni, in ma auren zaiyi ai ban hana shi ba, momy tace to ya isa haka yi shiru, abin da kara firgita ni shine duk wayoyinshi a rufe. Ya kira aliyu ya kai shi gidan ya umar amma maigadi yace musu ya dauki mota ya fita, kwana nayi kuka damke da takarda a hannuna. 143-Da safe kam labari ya kai gidanmu. Abba da alhaji a falo suna tattauna yadda za'ayi. Abba yace anty amarya ta kira ni suji ko saki nawa ne. Ta same ni momy tana ta min fadan kukan da nake ta ce ai yazo ma sai ya kara raina miki wayo. Gara ma ki daure ki nuna bai dame ki ba. A raina nace momy ba zaki gane bane, samun kamar ya umar zai min wuya. Anty tace su abba suna kirana shima ya umar din sunci sa'a ya kunnan wayarshi kuma sunce suna neman shi yanzun nan. Kizo da sakin saki nawa ne? Fuskata duk ta kumbura cikin kuka nace bansani ba. Na dauko takardar kan madubi da zanyi sallah na aje ta don hannuna ta kwana muka tafi har momy tana cewa muje zai ga fushina yau. Muna shiga yana shigowa, wani kyau naga ya kara min shigar kananan kaya ta kara maida shi matashin yaro ya zauna. Momy dake zaune kusa dani ta zungureni ta baya alamar wai in daina kallonshi. Na sunkuyar da kai can na kara kallonshi sai ya min gwalo. Abba yace yanzu umar abin da kayi yayi daidai kenan? Yace me nayi abba? Momy cikin fada tace ina fa zaka sani, shiyasa nace a caji kwakwalwarshi. Alhaji yace duk ba haka ba, yanzu ta kawo takardar saki nawa ne? Na mika musa. Abba ne ya fara dubawa, tsaki yayi sannan ya ba alhaji. A raina nace shi kenan uku ya min. Na kalle shi ina sabon kuka shi kam dariya yake yi. Alhajin ya mike sun maida mu 'yan iska ne ma yaran nan. Momy tace saki uku ne ko? Alhaji ya bata gashi ki gani itama ta mika ma anty amarya ta fita. Dariya naga anti tana yi ta fita duk sun bar mu. Na dauki takardar a hannun kujera in da anty ta ajemin na soma duba ko saki nawa ne? Sai naga ya rubuta: 144 “Ni Umar faruk na kara nunka igiyoyin aurenmu, ba saki ba yaji. Ina son matata shin tana sona?” Na mike ina kallonshi yana min dariya nima dariyar nakeyi fuskata ga hawaye. Ya iso gurina ya rungume ni na dan mihsi dukan shagwaba a kirji nace kai ko? Yace sorry kin son umar ko? Nace ina sonka sosai. Ta kofar waje muka fita ba tare da na koma cikin gidan ba muka je muka bude sabon shafin soyayya da rayuwa mai dadi. 145 Na fito daga cikin mr biggs ina tare da yarana, sayyida da sayyid 'yan shekara biyar suna dauke da kayan kwalama. Junior yana da saurin girma don ya kamo 'yan uwansa, sai yaron cikin da nake dauke dashi muka nufi gidan rahma. A hanya ya umar ya min waya ina dauka yace kin zama matar general gobe za'a tabbatar damu, sai ku shiryo kuzo akwai shagulgula. Murna ba'a magana. Ya umar yana da sa'a duk cikin wadanda suka samu wannan mukamin ya umar ne mai karancin shekaru. Gurin dinner ne mata suka so su minkwace don haka na manne mishi. Munsha dauka gurin 'yan jaridu da kuma tambayoyi. Ranar muna kwance wata number sai kiran min miji ake yaba dauka sai naga yana kallona. Ana sake kira na dauka muryar mace naji tana cewa don Allah ka taimaka min ciwon sonka yana damuna, nace sai dai ya kashe ki, miji nawa ne ni daya. Yace haba asmy yaya zaki kashe min kasuwa? Na harare shi na tashi xan fita ya kamo ni Allah ni naki ne ke daya, da ace ina kula mata da nayi goma yanzu. Na dube shi bana son kishiya fa kaji mijina? Zo muyi wata hira mai dadi ki bar batun kishiya ke kina wadatani baki hanani abin da zai sa inji sha'awar wata. Kina wadata ni, zokiji wani story kanwata. Yau asibitoci muka nufa don kai taimako ga marasa lafiya. Ya umar kan ware kudi duk wata uku dan taimaka ma al'ummar annabi. Yace yau zan rakaki asmy nima ina son samun ladan ziyara. Kai fa ke bada kudin gurin 'yan HIV, muka soma a bakin gdon wata mata na tsaya jin tana cewa soja, baiji ba nace ya umar, farida ta fita hayyacinta ta koma kwarangwal. Duk wannan kyan babu shi ya gudu, ta soma kuka tana neman gafara. Yace yau ga sakamakona kuma kinga yadda Allah yayi dake, dama kince da sannau zanga yadda Allah zaiyi dake. Ya fita nima na bishi. Ina dukiyar da ta tara? Ina iyaye da 'yan uwanta? Duk sunki ta da ko itace ma shanawa a dangi. Mu kam soyayya akalar rayuwa, dan iyaye sun miki zabi kada ki ki. So da yawa yana zama alheri. Tammat bihamdulillah. THE END!!! adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *