Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, April 3, 2017

FUTUHATU KHAIR COMPLETE

adsense here [11/10, 8:12 PM] ‪+234 809 308 3613‬: 🌹🌹FUTUHATUL🌹🌹 KHAIR🌹🌹 (August 2016) Na Xainab Y Hussain✍🏻 {Huum,wannan labarin qirqirarrene,ba'ayi dan cin fuska ga kowaba,kuma duk Wanda ya juyan labari *Allah ya Isah*} Aminci ya tabbata ga duk wanda ya karanta wnn littafin, sadaukarwa ga Daukacin writers baki daya. Episode 1 Assalamu alaikum, kina ina matar gidan nan?nasan kina d'aki fito kiban kud'ina ,haba ace kullum yarinya sai uban cin bashi sai kaxo karb'a alallameka da dad'in baki. Da fara'arta ta fito daga cikin daki,tace Adda Bena ce !sannu d xuwa kujera ta janyomata sannu ,ni bawani sannu gaskiya kud'ina xaki bani,murmushi Meime tayi tace dan Allah kiyi hakuri insha Allahu nan da sati xan baki wallahi maigidan ne kwana biyu ba ciniki shiyasa.kaji irin abin koh!nidai kawai sati na xagayowa xanxo na karb'a,shikenan Allah y kaimu, har Adda Bena ta fita sai ta dawo,Yauwa Miemi dama inason tambayarki wai me kikesawa a girkinki kullum unguwa sai ta cika da qamshi,dariya tayi tace maggin da kike siyarwa dashi nake amfani,Kuma ni tsayawa nake ina girki a hankali,Itadai Adda bajin maganar maganar Miemi takeyiba,miyaun tane yaketa tsinkewa tunda ta shigo takejin qamshi shiyasa ma bata tsawaita maganarta ba. Miemi tasan halin Adda Bena shiyasa tace xauna Adda na xubomiki tuwo ne ,nasan baci kike ba,da sauri tace la aini mutuminane tuwo kamar kuwa kinasan yunwa nakeji ,haka ta xauna taci abincin ta tasha ruwan randa,sannan ta miqe tace Yauwa sati kikace koh tace eh, Allah ya kaimu haka tafita ita Kuma takoma d'aki. Bacci yafara d'aukanta tajiyo sallmar megidanta Kabeer,da sauri tafito tana dariya tace Allah yau ka jima bacci har yafara d'aukana,turus tayi ganin shi da wata yarinya wadda batafi shekara 11 ba tayi baqi ga kayan jikinta sunyi datti,kallonsa tayi tace daga ina?dariya yayi yace before kice komai plx let her take a shower first, then sai kiyi complaine, kallonsa tayi tace banda ruwan d'umi" Kiyimata da nawa abinda yace kenan ya shiga d'aki. Wayyo typing wuya,plx mama Hassy or Maman Bobo come nd join me plx😜😜😜😜😜😜 © NAGARTA WRITERS ASSOCIATION© 2 u futha love *@ut@r h@jiy@*✍🏻 [11/10, 8:12 PM] ‪+234 809 308 3613‬: 🌹🌹FUTUHATUL🌹🌹 KHAIR🌹🌹 (August 2016) Zainab Y Hussain✍🏻 Episode. 2-5 ``✍🏻`Hannun yarinyar ta kama suka shiga toilet,sannan ta fita ta d'ebo ruwan kanta tafara wankemata saboda gaba d'aya qasa had'eda datti sunyiwa kan yarinyar sallama,hakan yasa gaba dayan ruwan yatafi gurin wanke kan,kadan ta rage wanda dashine tayimata wanka, hannunta ta kamo suka shiga d'aki kayan make-up nata ta d'auko mai tashafamata akan sannan tayimata kwalliya dai dai.``` *Huum! ko kefa keda kike son yarinya gashi Allah yabamu daga sama,kallonsa tayi tace hakane amma ya akayi kasameta?nifa banson kwashe kwashe dan Allah baibamu d'a ba,ai baya nanufin yamanta damu bane,komai lokacine.* ```Haba Miemi xanyi miki qaryane,Wllh kinji na rantse kwana wajan uku ina ganinta awajan,damagaran tana bin mutane wad'anda suka rage abinci tana ci,koni sai dana bata nawa,jiya kuma dawowata daga abalak naganta wasu suna dukanta wai sunsiya abinci kafin su wanke hannu su dawo ta cinye,ni na biya kud'in sannan nayimata fad'a na tambayeta gidansu tayimun shiru nayimata magana amma batacemun komai ba,shine nakaita gidan mai unguwa,daxu ina fita na had'u da mai unguwa yake cemun gaskiya yara sunyimasa yawa saboda haka nasan yadda zanyi da ita,haka na d'auketa muka tafi kasuwar tare,muka dawo tare kuma ,kinji yadda akayi na sameta``` *Hawaye ta goge tace Allah sarki yarinya kyakywa komai ya fito da ita daga gida ko kuma bata tayi Amma kuma kamar ba 'yar qasar nan ba,dan batayi kama da 'yan Niger ba,tafi kama da Larabawa ko Fulani,wallahi nasami 'ya,hannunta ta riqo tace ya sunanki baby,kallonta kawai tayi ganin haka yasa tayimata alama da hannu ya sunanki,itama da hannu ta rubutamata sunan ta BILKISU.* Kallonsa tayi tace ko bata magana ne,kai ta d'aga masu,Allah sarki insha Allahu zan riqeki kamar 'yar dana haifa,Shimi ta d'aukomata tasa mata,sannan ta zubamata abinci da kanta take bata har ta qoshi,sannan sukayi alwala sukayi sallah. *Wacece Miemi da mijinta Kabeer* *Miemi matace gurin Kabeer auren saurayi da budurwa sukayi,shekarar su shida da aure Amma Allah baibasu haihuwa ba 'yan Nigeria ne,garin Maiduguri,Miemi ta kasance mace mai hankali da mutunci batada hayaniya kyakyawar gaske batada abokin fada kowa natane mjinta dai dai gwargwado yana kulawa da ita komai takeso yanayimata batada k'iwa ko lalaci kaf unguwarsu ansanta wajan iya sarrafa girki,tana iyakar qoarinta wajan kula da mijinta,basuda shi sosai amma sunada wadatar zuci,mijinta d'an kasuwane sannan kuma ayanxu yana neman aikin gwamnati Ba inda baijeba amma baisamu aikin ba, kuma ga kasuwar yanzu bata ci sosai, dalilin dayasa kuwa lokacin daya saro kaya daga Nigeria zuwa Niger Allah ya saukar da lbtila'i akan kayan babu abinda yayi saura akayansa,wuta ta cinye,wannan dalilin yasa ayanzu abubuwa sukeyimusu wuya duk da haka bazaka je gidansu ba karasa abin sawa abakinka, ba,gwanace wajan iya sarrafa turaren humarah,da turaren daki,tanasamu dai dai gwargwado.kasuwanci ya kawosu qasar Niger,suna zaune a garin abalak,ita da mijinta* ®NWA® _Jinjina gareki Namecy ta Xee Maman Khady._ *2 U Futha Luv👯* *@ut@r h@jiy@*✍🏻 [11/10, 8:12 PM] ‪+234 809 308 3613‬: 🌹🌹FUTUHATUL🌹🌹 KHAIR🌹🌹 ( August 2016) @ut@r h@jiy@✍🏻 Page 5 - 10 ```Janyo BILKISU tayi jikanta,tace kiyi hakuri bansan komai ya fito dake gida ba amma insha Allahu nixan zamemiki UWA,kinji BILKISU, kai tad'aga alamar to!.Dawowar sa daga masallaci kenan,ko gida baishigaba yaji anmasa sallama amsawa yayi had'e da juyowa,a'a Alhaji ne sannu ina yini'malam Kabeer ya gida da iyali,alhamdulillha yace,Alhaji yace wato gaskiya nayaba da hankalinka kuma dama nadad'e ina San ganinka wato rumfata ta kasuwa,nasan kasan tafi shekara da rifeta dalili kuwa baya rasa nasaba da irin ta'adin da akayi mun,shine nakeso Idan ba damuwa mezai hana ko gobe indai ashirye kake kaxo kaganta Idan zaka iya jurewa xan d'oraka akai saboda tafiya xanyi Kuma Wllh babu wanda nayadda dashi kamar kai,Kuma koda xaka xuba kayanka aciki Ba matsala, fatana ka riqe gaskiya,kaje kayi shawara gobe da safe naji yadda kukayi,Allah yabamu alkhairi,abinda yace kenan ya tafi. ``` *Da sallama ya shiga gida Miemie ya tarar ita d'aya,kallonta yayi yace duk jiranane haka,to gani na dawo,ko kallonsa batayiba,tace haba dan Allah wannan wane irin hali KA tsiro dashi, naji daxu saboda BILKISU ka dad'e yanzu kuma saboda wa kajima?hum Miemie kenan Wllh ana idar da Sallah natawo Alhaji RAHEEM ne ya tsaidani,wani Alhaji Raheem din,mutumin dabaya kula kowa shine zai tsaya yimaka magana,kawai dai ni nasan bazan juri wannan sabuwar halayyaarba,Shikenan amma ya inamiki magana kina magana haba dan Allah wallahi abinda kike zargina dashi ba haka yakeba,me xanyi da wata Seemby yarinyar baqa da ita,gani da kyakyawar mace agida ina zan tsaya kula wata Seemby,itace dai take sona, amma ni kece tawa,so don't be compuse fell free I'm Ur's, no more add any wife again insha Allahu ,u ar OK agurina,Huum to ya kukai meyacemaka,Yauwa Matata,kince in xauna dai baxaki barni atsayeba,dariya tayi hannunsa ta kama tace Idan ma acinya kakeson xama bismillah,wa rufan asiri karna karyaki inrasa ina xankai larurata,barni dai inxauna a qasa,suduka sukayi dariya,nan dai ya labartamata yadda sukayi da Alhajin,yace to mekike ganin xancemasa Eh ko A'a?,Nidai banda abin cewa sai fatan Allah yasa shine FUTUHATUL KHAIR dinmu,(mabud'in alkhairi) Ameen yace daga nan suka tashi wanka sukayi sannan ta d'auki BILKISU suka shiga daga ciki.* Safiya nayi bayan sunga al'adar dasukeyi,ya shirya yace Miemie ni yakamata naje,ko shine xaiyi kirana,a'a kai zakaje tunda lokaci yabaka yace Idan ka amince sai kaje kayimasa bayani,Allah yasa alkhairi, Ameen yace.Yauwa Miemie Idan BILKISU ta tashi wane kaya xatasa,ko kafin ta tashi ki wankemata nata ,tav nifa Wllh a shara nasasu,sun yayyage,to! Yanxu ya xa'ayi?au Allah yasa Lokacin da Aunty Hassy taxo tamanta kayan babynta har kala 3 bashine nakewa indi xakaje katafi mata dashi,yanxu kuwa BILKISU tasamu kaya.kayi sauri 8 hartayi,plx kayi addu'a Allah yabadadinki*,Ameen yace sannan ya fita. Tunda yafita taketa addu'a Allah yasa wannan abin yaxamo solar arziqinsu,Haka tayini tana addu'a,lokaci lokaci tana duba BILKISU amma ko motsi batayiba,wajan 2:30 ne tayi juyi ,ganin haka yasa taje tanad'an buga bayanta wai ta tashi, kafin ta tashinne taji wayanta da sauri ta d'auka mijintane da sauri tayi picking hamdala taji yayi yace Miemie Allah ya amsa addu'anki Wllh har kayana yace da d'akko dama Kuma sauran sati biyu kud'ina suqare na hayar teburin,yanxu kuwa kinga abinci ma harda rabin kaza,aka kamun nakasa ci,tunani nake mekikaci keda 'yarki?,dariya tayi me had'e da qwalla tace kajika,ninaci abincin na qoshi kaine dai baka ciba,'yata Kuma sai yanxuma tayi juyi,tashinta dai xanyi yanxu,a'a kyaleta kinsan kwana nawa tayi ba bacci Sai Allah to ki kyaleta ta tashi dan kanta,kawai dai kiringa juyata,sai na dawo mexan siyamiki,kinga yadda naketa ciniki,Kuma yace Idan na qara kud'ina afarashin dayaban nawane kud'in,na riqe Wllh bakiga ba kamar na shekara ina ciki. Allah dai yasa albarka,Ameen. ®NWA® *2 u Futha Luv* *Maman Khady sannu da typing ,Allah yabar qauna ,Ayiya yar basaja kema sannu,Hassy ,Sahaf ina gaisuwa, Anker hala pharm yayi seezing phone dinki* 😜😜😜😜😜 [11/10, 8:12 PM] ‪+234 809 308 3613‬: 🌹🌹FUTUHATUL🌹🌹 KHAIR🌹🌹 (August 2016) @ut@r h@jiy@✍🏻 Page 11 Ajiye wayar tayi,hawaye ta goge,tace ya Allah kasa wannan yarinyar tanada rabon ganin danginta,Allah ka bawa mijina abinda yaje nema,janyota jikinta tayi, ahaka itama bacci ya d'auketa.Sallamar dataji ne tayi salati sannan tafita waje,Adda Bena ce da *Maman fadeel*suka shigo lale Bena ce sannu ku shigo Wllh bacci nakeyi,sannu, *Maman fadeel* ce ta tab'o Bena tace amma gaskiya wannan matar 'yar gayuce kinji gidan qamshi,lallai dole kice ga inda xa'ayi mun had'in humrah,tana turaren wuta,ke babu abinda batayi,tafiyar ta sukaji da sauri suka canja hira. *Ruwa ta kawomusu da alkaki* zama tayi suka gaisa,sannan Bena tace kinga wnn 'yar uwatace a katsina take,aure ya kaita Ghana,yanxu biki zasuyi jiyan nan tazo take cewa Maiduguri zata za'a had'awa amaren Turaren d'aki,shine nace mata basaita wahala ba akwai maiyi,yanzu muna son kwalba *goma sha biyar*amaren uku ne sannan da kwalbensu xaki had'a nawa xa'a baki, ajiyar xuciyata ta saki tace Bena ko nawa kikawo xanyi, bakwason gishirin wanka,ahaf komai xaki had'a fatanmu yayi kyau da qamahi ,karkuji komai insha Allah xanyi yadda kuke so,tom Ga deposit kafin ki gama xa'a ciki, *dubu d'ari*suka ajiye,Ita kuwa Ummu fadeel gaba daya Miemi ta burgeta yarinya da ita amma ta iya gyara kanta. Fitar su kedawiya tajiyo motsin BILKISU da sauri tayi cikin d'akin hannunta ta kama brush tayimata sannan wanka,abincin ta ta d'akko abaki take bata,tana janta da wasa har suka gama. Rayuwa sabuwa komai yayi farko xaiyi qarshe,yanxu su Miemi basuda matsala komai ajiyewa Kabeer yake,gashi Kuma sunsa BILKISU a makarnata,komai suka tava alkhairi yake zama,Idan kaga Miemi baxakace itace ba, rayuwa sabuwa,Kullum basuda abin qauna da tunani da dubawa Sai BILKISU, sukance wannan yarinya itace mabudin alkhairinmu,daga nan suka sa mata FUTUHATUL KHAIR. ® NWA® *Ummu fadeela, Xee Mamsn khady ,Sahaf ,qauna zallah,Allah yaqara had'a kanmu* 2 U *FUTHA LURV* [11/10, 8:13 PM] ‪+234 809 308 3613‬: 🌹🌹FUTUHATUL🌹🌹 KHAIR🌹🌹 (August 2016) Na Zainab Y Hussain✍🏻 Page 12-15 ✍🏻Shekara kwana gamai yawan rai,yanxu FUTHA shekara ta biyu a qasar Niger,rayuwa yayimata dad'i kyanta da farinta kullum fitowa yake,ayanxu haka tana aji uku a qaramar secondary schoo,da taimakon Alhaji Raheem yasamu akayiwa futha primary certificate.Allah mai baiwa gata da qoqari,komai aka tambayeta xata bada amsa dai dai,amma da rubutu,tunda babu bakin magana,Maruqiyarta kuwa,Meemi babu abinda yacanja gameda yadda take kula da Ita. Lokaci da dama suna xuwa gida Nigeria, danginsu Meimi sai san barka,sun d'auketa matsayin jika ko 'ya,amma 'yan uwan Kabeer kuwa duk lokacin da sikaje,da kuka take dawowa,saboda komai nasa since akan matarsa yake qarewa,da 'Yar tsintuwa,itakuma ba haihuwa saidai taci,ta kwanta,addu'ar Miemi da 'yarta FUTHA bai wuce Allah yabawa Auntyna baby ba shiyasa a unguwar ake sonta, batada hayaniya,yaro duk qazantarsa tana daukan shi, kuma batada rowa,had'in turare kuwa,ba Wanda bata iuaba tanda karambani wajan iya abinda bata iyaba abinci kuwa indai ba makaranta itace take yi, batada fushi, Idan kaga fushinta,to akan anhanata aikin gida ne,kamar wanke wanke ko shara,tunda yanxu sunada almajiri,shi yake komai,Ita tafi son tayi komai da kanta kamar yadda taga RASH agidansu itace kewa hajiyansu komai,amma Ita QURRATU AYN batada aiki saina danna waya,shiyasa bata qawa da Ita. Duk da bata magana,amma haka ta keda qawaye sosai, dan lokacin da sukaje Nigeria,kowa sonta yakeyi,amma tafi riqe sunan,CANDY da KHAIRAT (panisau),saboda sune suka ringa kulata,har islamiyya tare suke tafiya,FIDDAUSI sodangi ce kawai bata kulata,shiyasa ko sunje bata ma zuwa indai take. Tunda safe ta tashi wanka tayi,ta d'ora girki,harta gama Aunty Miemi bata fito ba, shiru shiru,ganin haka yasa tayi tafiyarta tunda before ta kwanta bacci Abban ta kebata kud'in break,yaudai gata nan ne,coz of she doesn't see her Aunty, shiyasa take so silent, even taking lesson in the class she can't stay to understand what d teacher do for us, tunanin ta one,meyahana Aunty fitowa,har aka fito break she's not fell well ajikinta,RASH ce taxo ta xauna dafata tayi, da sauri ta jiyo,tana share hawaye,alama tayi mata,me ke damunki,fad'amata tayi,murmushi tayi,tace yanzu ke dan kawai bata fito ba, shine kikaxama lazy yau,Abbanki ya fito tao,Kad'amata kai tayi,alamar a'a,dariya CE ta kwacewa RASH tace ke banda abinki, mata natare da mijinta,dan basu fitoba,shine xaki shiga damuwa,Plx kiyi shiru lafiyanta lou,bacci maybe ya kwashe ta, amma nasan badan bacci ba,da xata fito koh,kad'amata kai taqarayi,yauwa to kiyi shiru, yanxu tawo muyi break kinga yau masoyinki nayi miki,d'an malele,da sauri ta tashi tana dariya,wushiryarta me kyau ga dimple d'inta dasuka qarawa fuskarta kyau,yauwa yi sauri kada ANEE taxo kinsanta cinye duce,haka suka xauna,Rash namata magana mai dad'i har aka tashi. Da saurinta ta shiga gida,Aunty Miemi tagani akwance ga robar miyau agabanta,da gudu taje tayi hugging d'inta,tana shafa kanta,alama tayimata,cewar bakida lafiya,?kai da kad'a,tace FUTHA banda lafiya,nadad'e inajin motsi acikina,jiya Kuma banyi bacci ba,kinsan tun kwanaki nake cemiki,abinci nake yawanci,bansan meke damunaba,ko wani abun ne acikin, shiyake cinye abincin bansaniba,hannunta ta jijjiga,ranar dai daga 'Yar har uwar akwance suka yini,sai da magrib ne da Abban ya dawo, yagansu ahaka, shine ya rarrashesu abinci kuwa kad'an FUTHA ta iyaci,Miemi kuwa ai Har saidata qara d malt,sannan taji daidai.Safiya nayi kuwa,asibiti suka tafi,gwajin farko doctor ya tabbatar musu da shigar ciki har wata hud'u,farinciki,murna ko ban fad'aba su suka SAMI matsuguni axuqatan wadan nan bayin Allah, kabbara kawai yake,Miemi kuwa kamar amafarki takejin wai ciki gareta. Xokaga d'oki daga uban d'an har FUTHA, family d'insu ma,murna suke,aure shekara bakwai,sai wannan karan Allah yakawo rabo,cikinta nada wata takwas tafara musu wasu xantuka,sai ana xaune ,xata fara,FUTHA naso ni maitsawan rai ce, inga girmanki,naso Allah taban tsawan ran da xanganki da iyayenki,naso ni mai tsawan raice ace yau gani ga d'an dana haifa,naso nayi tsawan ran daxanga aurenki,Kuma naji miryarki,Tana fad'a tana hawaye, Idan tafara wannan maganar suduka kuka suke sawa,shi kuwa fushi xai kama, yace wai ke Miemi akan ki akafara ciki, ko akan ki aka fara haihuwa,daxakisa mutane suna farinciki da murna kixo musu da xancen da xai d'aga musu hankali,Plx ki dena Idan bahakaba Wllh xandena xama kusa dake,kalli yanda kikasa yarinya kuka,mudai kidena mana wnn maganar.Hannunsa ta janyo tace haba mijina wannan fad'a haka, nadena afwaan,ya hayatee, abin sona,farinciki na,mabud'in rayuwana, haken idaniyata,daga tafara xai sakko,suda suna dariya. Kwanceta Ita kad'ai ad'aki ,ciwo tajeji kad'an kad'an amma bata nunamusuba saboda yau ake junior candy nasu FUTHA, shima mijinnata sunada meeting da 'yan kasuwa,ganin ciwan bana qare bane yasa tajanyo wayarta,ta danna lambar Benaxiratu,one ringtone tayi tai picking nishi tajiyo acikin phone d'in,da sauri tajanyo mayafi ,tayafa shigarta gidan keda wuya naquda ta tawo gadan fadan,amma Kuma takasa haihuwa,bayadda batayiba,rubutu ta dakko tabata,amma INA kamar qara ciwo ake, bankad'a labulena da akayine,yasa sukayi saurin juyowa FUTHA ce,ganin Aunty ta a wannan bad condition d'in yasa tafasa kuka,tana birgima,Allah yasa itada sabuwar qawar datayine,'yar shugaban makarantarsuce,HAUWA JABO,itane tashiga tambayi me tagani,alama tayi mata cewa mamnta take labour, kuma Abbansu baya nan,da sauri JABO tafita ,tace Allah yasa AUNTY YABI bata tafiba. *2 u FUTHA LUV* By *@ut@r h@ji@*💐✍🏻 [11/10, 8:12 PM] ‪+234 809 308 3613‬: 🌹🌹FUTUHATUL🌹🌹 KHAIR🌹🌹 { August 2016} (10:40pm) *Zainab y Hussain* Episode 16 A d'ari ta fita.Gudu Jabo keyi sosai batajin ma nauyin jikinta saboda kada *Aunty YBK* ta tafi,don taji tace daga makarantar sai airport dan dama kwananta biyu da sauka daga Ethiopia, ta tsaya a Niger ne gurin qannenta dasuke skul,a Niger, Sahaf da munay tunda sunmata waya cewar zasuyi junior candy, hakan yasa ta sauka a Niger, sun had'u da Jabo dan dama sunsan juna sosai. sauri Jabo take yi, dan akwaita da tausayi lokaci d'aya taji FUTHA ta kwantamata arai,kuma bayan haka ma ganin halin da mamanta ke ciki yasa taqara tausayamata,shigar ta filin makarantar keda wuya taga tashin motar Aunty YBK, hannu tasa aka tace *Inna lillahi*Ya xanyi ta tafi,kuma gashi ban kula da asibiti a hanya ba,dafata taji anyi da saurinta ta d'ago murmushine ya kufcemata,ganin Maman Ibrahim tsaye ,kallon Jabo tayi tace me kike anan,da tuni na tafi ,Sai naga 'yan NAGARTA kinsansu da xumunci Rash suka zuwo itada khadeeja candy murnar junior candy nasu,da sauri Jabo tace aunty YBk Plx save FUTHA mum,she's labour, tana magna tana janyo hannunta,haka suka tafi. Da saurinsu suka shiga gidan,ganin Bena sukayi a tsakar gida Jabo ce tace hajiya ina mai naqudar basuji amaartava fadawa dakin sukayi a wahalce suka tace haba,jama'a bafa birgewa ceba ko juriya ko Kuma ace kai ka haihu kai kad'ai a d'aki yakamata mata kusa ni Wllh haihuwa kai kadai tana janyo maka babbar matsaka ,bakasan yadda xataxomaka ba,yanzu gashi nan daga gani kin dad'e kina labour,Aunty yanzu ba time ne Na magana b save her Plx,Hauwa yanzu ban iya mata komai dole sai anje asibiti alfarma d'aya xan iya xuwa komai xa'ayi ayi dani. Fitowa sukayi tambayar Bena sukayi inane asibiti mafi kusa OPITAL shine na kusa amma wallahi Aunty baxasu karb'ekuba dan basuda kirki"mudai kikaimu Dan Allah haka suka sami mota har xasu rufe saiga FUTHA da rubutu a hannu d Ita suka tafi.Motar Na saukesu Allah ya taimakesu anturo gado,shine akasata bin bayansu sukayi atsakiyar cikin reception aka ajiye gadon ga Miemi sai kuka take danma Ita batada hayaniya Kuma batada raki da ihu irin namasu haihuwa,Aunty Yabi CE tace wa wata nurse sister Plx where is d doctor, kallonta tayi tace HAJIYA sai hakuri dan doctor ta tashi indai 3:30 tayi to bata qara ganin kowa tana cikin fad'a mata Sai gata ,yauwa gata nan ma gida xata tafi,juyawa tayi ido biyu sukayi da sauri doctorn ta qaraso tace Aunty YBK yau kece agari,me kikaxoyi Niger,dariya tace lallai *Jameela Mohd Ali*kece doctor d'in Allah y taimaka,qanwata na kawo haihuwa zatayi kuma gashi kamar ta wahala so Plx kiyi admitting nata ,labour room aka shiga da ita,addu'a FUTHA kawai take tana Allah kasa Auntyna ta haihu,wayar Jabo ta ara babanta ta bugawa,bata tayi tace ayimasa bayani kafin kace me haryaxo,Kuma har lokacin haihuwa shiru, Jabo ce tace da mariqin FUTHA dan Allah malam,ahaka aka haifeta kalleta kamar Idan ta bud'e baki xakaji maganarta,Ayya yarinya ba'a haka aka haifetaba,aduniya tasamu ba inda bamujeba Allah baisa bakin ya bud'eba,har ruwan *Tanut* mun kaita tayi wanka dashi Kuma tasha komai na Allah ne wataran bakin xaibud'e,Ameen Jabo tace rufe bakunsu keda wuya,sister Xainab tafito (Maman khadee)da saurinsu suka miqe at are suka furta ta sauka ? _2 U FUTHA Luv_ *By @ut@r h@jiy@*💅🏻💅🏻💅🏻 ®Nagarta writers association® [11/10, 8:13 PM] ‪+234 809 308 3613‬: 🌹🌹*FUTUHATUL🌹🌹 KHAIR*🌹🌹 (August 2016) {8:30am} *Zainab Y Hussain* Page 17 ✍🏻```Maman Khady ce tace bata saukaba,amma tana kan gab'a insha Allah .Harta juya FUTHA tajanyo rigarta miqamata rubutun tayu ,Kabeer ne yace dan Allah kibata amma FUTHA ina kika amso,kwatance tayi masa cewa gidan su Maman haneep ta karvo,OK dama Kinsan tunjiya nake burin zuwa ,Allah yayi miki abarka, Jinjina kai tayi, minti goma yayi kad'an Maman khady ta fito tace ina kayan baby,dagudu ta miqamusu kayan Allah yasa Adda Bena tace a d'akko.``` *Basu dad'e ba aka fito da Babyn kowa hannu ya miqa zai amsa babyn ,kai masha Allah abinda kowa yake fad'a kenan qaton baby namiji fari tas dashi, Jabo ce ta karb'eshi itama tamasa addu'a ,AUNTY Yabi ce taxo ,ina Maman baby lafiya take,eh! lafiyarta lou tana resting room nan da 30 minutes xata iya tashi amma ta wahala Babyn ne qato kuma badan anzo akan lokaciba dole operation xa'ayi mata ahaka ma saidatasha ruwan naquda five Leda,amma yanxu da sauqi tunda bacci take.Alhamdulillah kawai Kabeer yake cewa, waya yaf ara bugawa gida ya sanarmusu ihu suke acikin wayar na murna gidansu Miemi ya buga yana bugawa qanwartace ta d'auka hartafara Maman biyu,dariya yayi yace Sodangi to d'an d'aya kuka samu qara ta saki tace Yaya it means aunty ta haihu ofcours yace mata ,saboda haka ki ban gift din fada miki danayi,Allah xanbaka amma turan Babyn nagani nasan dani yake kama,ina d'ana dani yake kama gadogon hanci ba irin nakiba,wah? Wallahi kasan nidai kyau aguna hardana saidawa,naji xan turo shikenan? Eh tace yanzu fa xanfara shiri na tawo kace ina gaidata,xataji ya katse wayar.* *Doctor Jameela*```ce tafito godiya suka ringa yimata,ba komai yiwa kaine ko ina gida Aunty Yabi tace naxo xuwa xanyi,Allah ya qara lafiya tace,Ameen haka tayi musu sallama, itama Aunty Yabi tafiya tayi godiya sukayi mata,tace Ba komai tare da Jabo suka tafi. _2 u FUTHA love_ ```By @ut@r h@jiy@💅🏻💅🏻``` *© NAGARTA WRITERS ASSOCIATION©* [11/10, 8:13 PM] ‪+234 809 308 3613‬: 🌹🌹 FUTUHATUL🌹🌹 KHAIR🌹🌹 (August2016) {4:00pm} *Zainab Y Hussain* *Page 18* ✍🏻Maman Khady ce ta dawo tace kuna iya shiga,tom yace gaba d'aya suka shiga d'akin Adda Bena ce agaba,sai ummul fadeela don taxo a lokacin Kuma kunsan Miemi tayimata had'in turare,mutunci datayimusu yasanya suka qulla qawance. Tare duka suka shiga da sauri FUTHA taje tayi hugging nata,sannan ta xauna kusa da ita kowa murna yayimata Allah yarabasu lafiya,babyn kamar mamanshi Kinsan Miemi da kyau Kabeer shima ba bayaba,kyakywane Babyn, basu jima ba suka tarkato suka dawo gida,gyagyara d'akin akayi har gidan tunda k'ofar gida xakasan gidan maijegone wadda takeji da gayu,dan turaren wuta akasaka ako ina,Bena andage anata aiki ,suna xaune ta shigo da flask da kayan tea had'amata tayi ,yauwa yakamata kisamu abi mai nauyi kici ko agirka miki, la Adda nayi girki d'azu saidai bansaniba ko xakuci dan gaskiya yayi sanyi,nibancin abinci Idan yai taking one to two hours balantana wannan dayajima FUTHA xoki d'oramana girki wannan Kuma abawa almajiri,haba Miemi ai wannan b'arnace bara muci shi ahaka ,d'akko ke FUTHA Idan yaso sai tayi miki naki,a'a tayi gaba d'aya kema axubamiki tunda bakiyi girkiba mai maigidan naki zaici ?ai kuwa dai tanayi tana loma,Adda Ba sauqi wajan xira abinci,flask guda suka cinye itada ummul fadeela, gara ita ciki gareta dan taci. D'oki bai bar FUTHA tayi bacci ba,minti kad'an ta tab'a yaron,qawayenta irinsu Rash,candy,Anee QURRATU haka sukayi ta xuwa balantana candy Ita kowa tafiya yayi yabarta,tunda taga and'ora abinci ta xauna,abinnema yasa mu gurinta,kwadayi wajan ta hardana saidawa. Maigidan kuwa gaba d'aya jinsa yake acikin wata duniyar abinda suka fidda rai gashi Allah yabasu saidai godiya ga sarki Allah. Xuwan sassafe 'yan uwanta danasa sukayi su Fido Sodangi ansamu new baby sai rawar kai take, Aunty Jidda da Mrs omar ba xama gyara nan gyara can,Afreen ce tace Aunty Nafeesa ina Mama wacce mama,Aunty Hassana (Hassy) nake magana kaddai bada Ita kuka zoba?au kinsan tanada qawa a Niger gidanta tafara sauka wai tace ta kawo kaya xataje ta duba,au Maman Bobo kike magana yauwa ita,ok tace . Tun safe FUTHA suka fita itada Abban ta siyowa baby kaya, batada masaniya a xuwan su,da murnarta suka shigo gidan,d'akin tax big ata shiga ta shiga kan cinyarta ta d'ora kanta,twasa taji abayanta ke dallah d'agata qatuwa dake,Allah Miemi wataran sai kinyi nadamar riqe wannan 'yar,kalleta dan Allah "Mrs Omarce tace haba Yar mutan Anker kekuwa meye ruwanki da Ita,naga alama ba kwa shiri dan waccan xuwan da sukayi haka kike mata,kefa kallone naki,itada 'yarta ko FUTHA?kai ta kd'a 2 u FUTHA Luv *by @ut@r h@jiy@*💅🏻💅🏻 _® NAGARTA WRITERS ASSOCIATION®_ [11/10, 8:13 PM] ‪+234 809 308 3613‬: 🌹💐FUTUHATUL🌹💐 KHAIR🌹💐 (August 2016) {7:00pm} *Na Zainab Y Hussain* *Page 18-20* ✍🏻```Haka Mrs Omar da Aunty Jidda Aliyu suka yima Anker magana badan tasoba tayi shiru dan dai tasan sune gaba da Ita,sallama sukaji daga waje,da sauri Fulani sadiya tafito daga ciki wa alaika salam jin maganar mace yasa Anker saurin tura kwanan abinci bed room,Seemby ce budurwa Kabeer, shiga tayi bayabo ba fallasa Miemi ta amsa,qin bata Babyn tayi saida tace muga Babyn, sannan tabata,shafa kansa tayi tace tubarkallah Babyn me kyau,masha Allah Anker tafad'a dan tasan rigimar da akayi akan Seemby,Maman FUTHA baby dai yahana kixo bikina next week ne Nigeria ma xani yau nace sai naxo naga babyn ,ayya bikinki xa'ayi Allah yasanya alkhairi sai hira ta b'alle atsakanin su,tunda taji baxata auren mata miji ba ``` *Biki buduri xoka ga uwar gayya Miemi tayi kyau baby yaci sunan Abdallah futha ce taxab'i sunan,nanma saida su sodangi sukayi magana Allah yaso magana batayi tsawo ba sosai. kowa kagani yaci kwalliya,duk inda kahanga taron mutane kake gani su Kansu 'yan Niger d'in garin abalak sunsan ana suna,komai anyi ya wadata,balantana dangin Miemi irinsu Rahina (mrs Aliyu) ansha kyau,'yan exellent sunxo sosai kodan sunsan xa'ayi abin kirki,Kuma gasu da kwad'ayai,NAGARTA ma sunzo Sanah tayi qoqari tundaga kano ta taho,kowa kagani yacika baki da nama kunsan Niger da nama kamar me,su Haneepa da mama Hassy sune masu rabo, ba wargi kunsan Hassy qatuwace shiyasa batada wasa,doctor Jameela ma taje,Jabo ma haka,Anker saboda masifarta su aunty Jidda suka hanata rabo,amma dai itace mai raba take away dasu Uumu Ruman*,```HAJIYA maiJidda Musa ,da Aisha humaira admin littatafan Hausa duk sunje``` *FUTHA itama danata qawayen party guda suke agidan Adda Bena,Aunty Miemi ce ta d'ibarmata komai,da sauri ta shigo batasaniba ta bangaji Anker mari xata bata Aunty Jidda ta hana,haba batasan ta bigekiba ran sunanma,FUTHA me kike so, alama tayimata kaya xata canja Miemi tace,Swiss ne me kyau ta d'akko tasaka iri d'aya sukayi da Aunty ta.haka aka sha suna lafiya da xaman lafiya kowa yaci ya qoshi,```Maman shaheed``` nagani tana sid'e hannu gurinta aunty Hassy taje tace bakisamu abincin ba? lah nasamu,wad'an cen ne dai basu samuba suwaye nagansu haka kamar yaqi,```'yan dandalin Autar Hajiya ne ```innalillahi amma yanxu sukaxo,mun shiga uku da masifar auta ,daga baya Aunty Mamu tace d'arima kika shiga dan Auta Ba dama,Kedai bari,Allah yasa yanxu muke magna anmanta buhu uku acikin d'aki da kulan paper kitchen maqut najiyo had'iyar miyau kallan wadda tayi nayi Hulle ce ,itada Fatima ,Ga Ameera da Maryam Cavara akusa dariya nayi nace tav amma Auta tahad'a mutane haka akayimusu goma ta arziqi* ```Anshare suna, Aunty Jidda Sune kan haba wajan irga abinda aka samu,wata atamfa aka d'aga,Sodangi ce tace wallahi wannan kalatace ,Miemi kuwa tace kalar 'yatace FUTHA saidai kizab'a awata ,haka dai sukayi hira irin Na 'yan uwan juna.Shirin kwanciya sukayi, FUTHA waje tafita tayi kwanciyarta,a tabarma,Miemi ce tafito ta ganta ahaka ,tashinta tayi suka tafi Kan katifa suka kwanta,3:00 dai dai FUTHA ta tashi fitsari Har ta kwankwanta,tajiyo nishi sama sama, sharewa tayi amma saita qara jin kamar qara yi ake tana juyowa Aunty Miemi riqe da ciki da sauri tayi kanta tashin su tayi baba d'aya jikinta ya jiqe da gumi kuka sukasaka FUTHA ce tafita takirawo Kabeer yana xuwa kanta yai yana Miemi yadai meke miki ciwo ,cikin ta ta nunamasa,,Plx kufito da Ita Na d'akko mato,hannunsa ta riqe ta had'a dana FUTHA,tace plx hayatee ga amanar FUTHA ka riqeta kasamamata kyakyawar rayuwa kayimata xab'i da miji nagari,Idan Kuma nasamu iyayenta kace ina gaishesu Allah baiyi nixan sadasu d 'Yar suba,kaji ka taimakan ga da'na kula dashi wani irin nishi tayi da sauri 'yan uwanta sukayi kanta No!``` Loading .....................21 *2 U FUTHA Luv* _@ut@r h@jiy@_💅🏻 ® NAGARTA WRITERS ASSOCIATION® [11/10, 8:13 PM] ‪+234 809 308 3613‬: 🌹🌹*FUTUHATUL*🌹🌹 KHAIR🌹🌹 *(August 2016)* *Na Zainab Y Hussain* *page 21* ✍🏻```Kabeer ne yatabata yaji shiru, aunty Jidda tace lafiya,asanyaye ya kalleta ganin idaniyarta na xubarda hawaye,bai iya cewa komai b,ya miqe ganin haka yasa Mrs Omar d Mama Hassy xuwa gunta da sauri,tatrabata sukayi suma,amma basuji wata alama wadda take nuna akwai rai atattare da ita ba.Anker ce tace Yaya Hassana matsa kugani,kinsan ciwan ciki yanasa mutum ma ya shiga comma, maybe kuma suma ne,itama dauriya kawai take,duk wani iyawarka da basirarka Idan kwana ya qare ba makawa Sai ka tafi,Allah sarki Miemi duniya lokacin datake qaunar xaman cikinta lokacin Allah ya d'auketa cikinta,lokacin da take burin gani Na sanyin idaniyarta,lokacin Allah yara basu, lokacin da d'anta yake bid'arta lokacin Allah ya amshemasa ita,Allahu akhbar Lokaci yayi,ganin dai dagaske ta amsa kiran ubangiji gaba d'aya suka fasa wani irin kuka,FUTHA kanta taje tafara jijjigata tana wani irin kuka mai tsuma rai,y'an uwansu ne sukaxo kanta da kyar suka banbareta ajikinta,so take tayi magana amma takasa,sai ayau taji tausayin kanta,takumaji inama tana magana,ganin d'aukanta ne yasa kowa kuka,'yan uwa akayi tabugawa waya,kafin safiya anmata wanka,qarfe 7:00 'yan uwa suntaru Fido ba'a magana saboda ta shaqu da Meimi sosai``` ****** ****** ***** *Haba d'aya 'yan uwa antaru masu karatu nayi masu laximi nayi,FUTHA itama Qur'an ta d'auka tana karantawa,qawayen ta suxo,Rash itace tafara xuwa sannan Qurratu da candy, Kabeer ba'a magana dan tunda yadhiga d'aki ko qafarsa bawanda yaqara gani,yana cikin d'aki kuka kawai yake yanxu Miemi ta mutu,dama Ba sonsa takeba,shiyasa ta tafi ta barshi,tun yana kuka har kukan ya qafe,saida lokacin kaita makwancinta yayi sannan akafara tambayar ina mijinta yaxo suyi sallama, haka babansa ma yace ina yarinyar datake riqewa haka FUTHA taxo nifa kanta tayi, akan gawar shima da yaxo kasa komai yayi,haka aka d'auketa,lokacin da xasu fita gaba d'aya aka rud'e FUTHA xubewa tayi bataqara Sanin kantaba sairan sadakar uku,haka ta tashi ganin yawan mutanen dake cikin gidan ya tuna mata da abinda ake,kuka takeyi,'yan uwan Kabeer sune suka rarrasheta,amma 'yan uwan Miemi ko kallo garama manyan.* **** * ****** ****** ```Yau akayi sadakar bakwai ayaune Kuma dangi suke shirin tafiya 'yan uwan Miemi Aunty Jidda itace ta d'auki Babyn,amma su bayau xasu tafi ba,'yan uwan Kabeer dai sune suka tafi,kafin tafiyarsu nan ne suka xauna ,akayimasa naaiha,sannan mahaifiyarsa tace Kabeerkasuwanci yakawoka Niger,har Allah ya axurtaka kayi aure ,bakada kowa a Niger saboda haka kayiwa Allah kabar garin,Kuma duk wani abu dayake banakaba kayi qoqari kasada shi damai abin,dan bansan kakai nan da sati biyu a garin dan xamanka baxai amfaneka da komai ba,tunani ma kad'ai ya isheka abinda KA Tara kataqo gida,Allah nikuma yabamu ikon riqe amanar da matarka yabaka ta wannan yarinyar.haka sukayi fad'a masa sannan suka tafi``` *Yau dai aka d'ebe komai Na Miemi Kuma 'yan uwanta mota biyu sukayi suka tafi,Sodangi kamar tace sutafi da Miemi kodan son datakewa sistern ta,Amma tasan baxasu yadda ba,itama FUTHA kuka take kamar tace xata bisu amma ba hali,haka duka tafi suna kuka,kamar yaune suka ka 'yar uwarsu amma gashi suntafi batare da itaba,ko tunanin dawowa,dominta ba,qanqame Babyn Hassy tayi, haka mota tana Sai 9ja.* *Gidan Adda Bena FUTHA ta tafi,anan take kwana ,shi kuma gaba d'aya yanzu komai nasa yake saidawa din har gidan Alhaji Raheem ne yasiya,Kuma gashi ayau sunyi bankwana dashi a komai, don ya bashi mukullin shagonsa,sannan shima yabashi sallamarsa.* *2 U FUTHA LUV* *by @ut@r h@jiy@*💅🏻 *NWA* ```Allah kabawa Miemi lafiya,Dan acigaba da Fannah``` *Welcome back home my lovly Freind, Hauwa Jabo* 🌹💅🏻 FUTUHATUL🌹💅🏻 KHAIR💅🏻🌹 *Xainab Y Hussain* *Page 22-25* ✍🏻```A yau tun safe suke shirin barin garin,gaba d'aya jikin su yayi xanyi,ita kanta Bena sai yau taqara jin mutuwar qawarta,haka tahad'awa FUTHA goma ta arziqi,gaba d'aya qawayen FUTHA sun fito domin rakata kuka suke sosai dan FUTHA qawace tagari mai kuma gudun fad'a da abin hannun mutane,Rash da candy sune manyan qawayenta Idan kagansu alokacin babu abinda xai hana KA zubarmusu da hawaye,saboda yadda suke kukan rabuwa da FUTHA.``` *Haka suka hau mota xuwa tashar Niger, asibitin da aka amshi haifuwar Aunty Miemi shi suka wuce kallon asibitin tayi hawaye ta goge axuciyarta tace kamar ba rana irin tayau aka kawo aunty labour Kuma tafito da qafar ta haka suka wuce gidan aminiyar Aunty duk inda suka wuce hawaye kawai take goge wa,inda kukanta ya qaru shine gurin Anee toilor wadda tare su kaje da aunty before sunan Abdallah, haka taqara saka kuka,hannunta ya damqe ahaka har sukaxo inda xasu hau mota xuwa Nigeria🇳🇬. Kallonta yayi yace FUTHA kina kukan rabuwa da Auntynki,?kai takad'a murmushi ya saumata wanda yafi kuka ciwo yace kina kuka na rabuwa da ita ad'an shekarun da kikayi tare da ita, kina kuka saboda yadda kika shaqu da Ita,kina kuka saboda yadda take kula dake take lallashinki ko ? kai taqara kad'a masa,kallonta yaqara yi yace to FUTHA kinyi kuka saboda haka,nikuma nayi kuka nida mukayi shekara sama da goma tare,why Miemi! meyasa kika xab'i ki horani ta hanyar tafiya ki barni,bayan kinsan kina sona nima haka.rungume shi tayi haka suka sha kukansu.* ```Hannunta ya matse yace FUTHA kiriqi amana duk inda kika shiga,ki riqe mituncinki da qimarki ta d'iya mace ki darajata kanki sannan xa'a darajataki,kiriqi Allah aduk inda kike, hawaye ne kexuba a idaniyarsa,Naxo Niger dan nema,naxo tare da Miemi duka da 'yan uwanta basu so tafiyata da itaba naxo Niger a banda komai nasamu abin kaina,naxo Niger tare da mahad'in rayuwana Miemi amma gashi xan barta batare da itaba,Allah kayimata rahma,gaba d'aya 'yan motar suma hawaye suke don tausayinsu,da qyar ya rarrashi kansa.``` *Tafiya suke wasu na bacci wasu na danna wayarsu,wasu na ciye ciye amma Idan kadubesu ba abinda suke Sai Jan carbi,yanayi yanamata nasiha da yadda xata tafi da rayuwarta, haquri jigone FUTHA kikasance mai hakuri da rayuwa,xaki iya tsintar kanki awata rayuwar daban,ki hakuri d yadda taxo miki, sun shigo gari sosai dan har waya yayi gida sun kusa sauka,Dan sauran baifi minti talatin su isa garin sokoto,wata mota ta tawo da gudu,ba yadda drivern beyiba dan y kaucemata amma ina Allah ya tsara, dan gaba d'aya motar suka gangara kafin kace me, sunkama da wuta,jama'a ne sukayi Kansu amma ina ko alamar tsayuwa wutar batayiba duk iya qoqarinsu saida motar kwana kwana suka xo,haka aka fito d mutane wasu sun mutu wasu da sauran ransu,cikin wad'an da suka mutu harda Kabeer,hankalinane ya tashi ganinb haka nace OMG!FUTHA yaxakiyi wannan qaddarar Allah ya d'oramiki,haka nafara raba idanu koxanganta amma duk hangena banga mai kama da itaba ma,INA tayi to?Waya d'auketa ban ganiba?kotanacikin motar haka natafi da sauri amma ko takalmi bangani nataba.Innalillahi wa inna ilaihi rajiuun"abinda nayita cewa kenan, duk hangena bangantaba ina tayi to kodai taxama qarwashi ko toka ?* *2 u FUTHA Luv* *® @ut@r h@jiy@*💅🏻 ®NWA® 🌹🌹FUTUHATUL🌹🌹 KHAIR🌹🌹 *©Zainab Y Hussain* *Page 26-30* ✍🏻``` Haka aka dauki gawarwakin mutane da yawa ciki harda kabeer,wanda wayar dake aljuhunsa Ita akayi amfani da Ita aka kira last call nashi,bugu d'aya aka d'auka Kabeer kun shigo garine ina 'yarta KA banjitaba tun d'axu.Am; Hajiya bashi bane to Waye?haka wayartasa ya yadda? Ba yarwa yayi ba,Mahaifiyarsa ce?eh itace lafiya meyafaru ko 'yan fashine suka kama su?Hajiya Accident sukayi ayanxu haka suna General hospital dake sokoto,Innalillahi wa inna ilaihi raji'uun! Yanxu muka gama waya dashi malam kafad'an gaskiya karkace d'ana yayi hatsari Wllh shi kad'ai garan namiji haba malam gaba d'aya tanayi tana kuka,haka ya kashe wayar shima hankalinsa atashe kuka shima yasa ka.``` *Haka tafito da gudu tana fad'a agidan,kan kace me jama'a sun taru,Hassy ce taxo dama tana gidan,kafad'arta ta riqe tace Mama me kike fad'a haka, kada xafin mutuwar surukarki yasa kiyiwa d'anki fatan matuwa,haba mama 2 hour ago mukayi waya dashi har yake cewa ya turo kud'inshi a account d'ina naga alert nace masa nagani, Amma xakice wai ya mutu kome?Basu gama magana ba Aunty SAHAF taxo da gudu ruqunqume Maman tayi tace mama wacce irin qaddarace taxo mana haka?wanda muke gani muji dad'i yanzu babushi,da sauri miss Hafsy ta mari bakinta,tace shegiya baki da burin daya wuce kixo kina ta yarwa mutane hankali, wani yayanne ya rasu ancemuku mutuwar kamar kashe kiyashi ne,wayar Hassy CE tayi ringing kamar baxata d'aukava ganin sunan mijinta yasa ta d'aga wayar,Hassana kina ina yanzu?ina gida kaga SAHAF taxo mana dawata magana itada Mama dan madai miss Hafcy ta buge bakin ta,Ita dai kawai burin ta yaga taro koma menene,yayan da daxu mukayi Waya dashi taxo tace ya mutu saboda rashin hankali . Ya akayi mijina kinga Hassy inason kusan cewa duk abinda Allah ya rubuta shiryayyene so kima daina d'aukan xancen su as joking, Allah yayiwa Kabeer rasuwa me kace?abinda kikaji na fad'a,wayyo Allah mutuwa mai ysnksn qauna kafin kace me mutane sun taru,haka aka tafi d'akko shi.* ```Jama'a sun taru,Kabeer Kuma sai dai tarihi,haka aka fito dashi likkafanin duk jibi,saboda buguwace akai jinin bai tsaya ba,'yan uwan Miemi sunji duk haka suka tawo dasu akayi komai. Mutuwar 'yar uwarsu sabuwa tadawo musu,har aka dawo gida shiru, ina labarin FUTHA? Fita xanyi Dan d'akko muku labarin ta Sai kawai naga wasu yara su,tundaga waje suna kuka haka nabisu nace to wad'an nan daga ina?magana naji abayana Ummi ce da Rash suka ce Auta ai indai bakiga wad'an nan gidan (xaman makoki Ba)to Allah baisa sunsan anyu mutuwa ba, nace ikon Allah sudai ayi mutuwa,ban rufe bakuba naga wata mota da dogarai kusa da ita,kayan abincine da juice sai Kuma kuloli nace ikon Allah haka gidan (xaman makoki) ya xama wad'an nan mutanen daga ina,Baba Habu ne ya fito gaisawa sukayi daga nan yace daga ina haka,gidan Su Hassana (Hassy) ok gidan marigayi d'an sararin kano Allah kayimasa rahma,Allah shima kakai haske qabarinsa Ameen sukace.``` *Kabeer anxma tarihi, haka hajiyansa ke fad'a,kanta ta d'ago da sauri tace Jama'a anzo da FUTHA bangantava,kowa kuma saiyafara raba ido ko mai kama da uta babu, Lallai duniyar wata biyu da suka wuce Idan kaga mamatan nan kamar ka d'auke su dan sha'awa yadda xakaga sina kula da junan su gashi an wayi gari babu ko d'aya yarinyar nan itama tabi mariqanta,yakamata aje asibitin agani ko xa'a ganta haka aka tafi an duba ko ina ba'a sametaba,addu'a sukayimata itama.* ```Abinci ake ci haka na hango yaran nan kowacce ta lemuka a hannu Ga bakinsu cike da naman kasuwa sunayi suna sawa awata leda,lallai duniya masu ci daban wad'an da akayiwa mutuwa daban.'yan groups- groups Na WhatsApp duk sunje Kowa kagani shima abinci yakeci NAGARTA ne kawai a nutse abinda yakaisu shi sukayi dasu d Musha karatu Na Aunty YBk,dandalin auta maciya kuwa harda masu guzuri,duniyar makaranta Na Ummi Aysha suma sunje Dan Nana Hawy itada Pharty abin ba'a cewa komai da flask suke yawa haka su cika suka tafi.Su dai tasu taqare sai mu.``` *FUTHA motar Na gangarawa door d'in motar ta bud'e su biyu ne suka fice haka sukayi ta gangarawa kan Sune yadaki da bishiya anan suka sume basu qara Sanin kansuba au bayan kwana uku haka suka farka Allah yayi taimaka basuji ciwo ako inaba,haka suka tashi itada wani yaro ya guemeta tafiya suke Ga qishirwa Ga yunwa haka suka fita titu ganin ta JUYA yasa yace mata baiwr Allah ina xaki ko kingane gida kai takad'amasa a'a,to inxaku Bini kitaqo Ni wanne wanne nake a kasuwar garin nan in kinsan bakida kowa ki biyoni ko Allah xaisa tabaki AIKI,inkuma xaki gane gida to dan naga kamar baki magna kai ta kadamasa.haka suka tafi mota suka tsayar suka shiga,suna tafiya taga antsaya tambayarsa tayi meyasa aka tsaya cemata yayi _Alhaji Abdallah mai nasara_ ne shugabna 'yan kasuwa da siyasa nagarin sokoto,Mutum mai kirki mai jama'a gason talaka ,Allah yasakamasa da alkhairi Ameen tace daga haka suka wuce.* *Wacece FUTHA* _Loading............. 31_ *2 U FUTHA Luv* *@ut@r h@jiy@*💅🏻 ® NWA® [11/10, 8:13 PM] ‪+234 809 308 3613‬: 🌹💅🏻FUTUHATUL🌹💅🏻 KHAIR🌹💅🏻 *©Zainab Y Hussain* _page 31-35_ ✍🏻```Alhaji Omar mutum ne mai kirki da son jama'a ,Allah ya bashi train dukiya daga cikin qasar nan da wajanta,Hajiya Lubabatu matarsace wadda sukayi auren saurayi da budurwa,'ya'yansu biyu mace da namiji. Suntaso cikin hankali da tarbiyya duk da kasancewarIyayensu masu rufin asiri, Macen Aunty Ameena anacemata meenah tayi aure da mijinta shima babansa mutum ne attajiri,sun had'u a qasar rasha inda take karanta Ganycologeis,shima yaje ganin doctor Aiman yakai mahaifinsa saboda qafar datake damunsa,anan duka had'u hira tayi hira sukasan cewa sud'in 'ya'yan abokanan iyayensune,Meenah amma fa ina xuwa gidanku,dariya tayi tace nima haka,dan Idan Pharty tana gida INA yin at least two weeks agidan,tsaya kardai kece Meenahn Pharty danaji kullum maganarta meenah murmushi ta saumishi,wayanta ta d'aga one ring Pharty ta picking qawalli ya gida lfy Lou,kinganni da yayenki haba,dama bakisan shiba ya akai kuka san juna Har kikasan broth d'inane,hhhh yaga 'Yar kyakyawar shine ya maqalemun,Wllh yaya yafiki kyau, haka kikace tao shikenan, wace ni ai kinfisa kyau,haka suka qulla soyayya tana gama karatunta akayi bikinsu,yanxu haka 'yayanta uku,Qaninta Kuma Abdallah yarone matashi mai hankali bashida hayaniya komai nasa ix so simple duk inda yaje abinda yakai shi shiyakeyi,bashida budurwa dan karatunsa ya shine gaba da komai a guns a.Qanin mahaifinsa Alhaji Sadam mutum ne mai arziqi shima 'yayansa goma maxa uku mata bakwai rayuwar outside ake a gidan ba ruwan su da kowa abinda yake gabansu shine dai dai ubansu baya musu fad'a koda agabansa sunyi badai daiba,Kuma ba'a kamasa qarar 'ya'yansa,maxan suma rayuwa suke any how, Mamansu ba ruwanta da irin shigar da zasuyi,kud'i kuwa ba'a magana baban su yabasu samari su basu, duk wannan arziqin da Allah yayimasa baya gani Na d'an uwan shi yake wa baqin ciki, shiyasa ko 'ya'yansa baa zuwa gidan``` *Guda ce daga cikin su mai xuwa badan komai itama take xuwaba ,saidan Abdallah tana masifar sonsa,Dan da babanta yace Sam baxai had'a xuri'a da wansa ba matarsa tafi qarfin shi kuma yaron bashida kirki ko xuwa gidansa bayayi,Kuma bashi yake son ki ba kece mai son,to ahir d'inki,Uwarce taxo tadafa kafad'arsa tace Abban Chuchu ninace tanemi soyauuar Abdallah saboda me kaji hauka,saboda kasamu KA cima burinka ta haka,Kuma kasan d'an shine komai nasa ayanzu,Idan bahaka ya xamuyi musami abinda mike so, Kuma kaga matarsa ba harka mukebe,'Yar ce tace mama Kuma ai duk da haka sai mun had'a da gidan boka jamjiri,dariya ya kece yace tab gaskiya mata Sai abarku ,ni bantava wannan tunanin ba, Amma ke Chuchu xaki iya,ko kibari ASA qanwar ki Ummi Dan naga tafiki iya abubuwa,hhhh lallai Alhaji ai Chuchu babu abinda naxata iyaba,to ni xansami Yaya nace yakamata mu qarfafa xumunci ko itace xatayi fighting akan haka, no leave her to do with her own idea, OK Allah yabada sa'a Ameen dady.* ``` Abdallah yau tunsafe yake shiri xai tafi Libya gurin abokin shine tare sukayi schools both Islamic nd mordan,a Nigeria suke shida Maman shi Kusa da gida suke tare suka tafi Cyprus har gama school masu tare, two years ago ne iyayensa suka koma Libya dama 'yan canne,Qanwarsa ce ta rash shine xaije masa ta'aziyya.Sallama yayi da iyayensa daga nan yaboya gidan aunty Meenah,haka yatafi airport jirgi ya Lula dasu samaniya.``` *Tafiyar awa uku cur takaisa Libya, Waya yayima Adnan ya sauka,haba dai yanxu kana ina ina airport OK gani nan,ten minutes kawai yayi yaxo rungume juna sukayi,yah Mai nasara kaxo lafiya?fyn oo ya hakuri Kuma Angode Rabbi samawati,mota duka shiga,cikin gidan suka shiga gaisuwa yayi musu suka fito waje,dare nayi coffee suke sha yace mai nasata wai yah haryanxu bakaga wadda ai match da kaiba,kit ninacemaka sai wadda tayi match dani,kawai lokacine Idan Allah yaso ko yanxu Xan iyayi, Amma Ni banda wani hope akan komai indai macace.OK !Allah yayimana nanalkhairi Ameen sukace tare.two weeks yayi a garin Kuma yau yake shirin tafiya Sai lallabashi yake plx abokin KA qara ko two days ne,kaga banyi yau Xan tafi OK naji xoka rakani cikin university d'in can,tom muje ,sun shiga cikin School d'in bajimawa suka fito,duna shirin shiga mota sukaga wasu motoci left and right the other kuma a middle nasu gab da capteria suka tsaya, qafa kawai yagani tasha lalle ja ga 'yan yatsun kuma da baqi,haka kawai taji yanason ganin wacece wannan yarinyar gaba d'aya ta fito doguwan rigane jikinta yellow tayi rolling da blue mayafi takalmi da jakan suma blue Ga hannunta yasha gold tafiya take a hankali table tasamu ta xauna,tab'o shi adnan yayi yace Abdallah, hala kaga choice d'inka,murmushi yayu yace wllh haka kawai yanxu nayi wani feelings akanta,amma tafi qarfin,daga gani 'Yar wani ce.Tabbas kuwa 'Yar wani ce amma yadda kad'auketa ba haka takeba.* ``` Zainab axxad kenan 'ya ga vice President na qasar nan su shida ne gurin iyayensu maxa hud'u mata biyu,da yayarta tana auren d'an gidan president kaf sunyi karatunsa a outside itane kad'ai tayi karatunta a wannan qasar sai Kuma Al-axhar ta madina anan tayi degree akan tafseerul Qur'an, tanada kirki batada kace nace Idan har mutum ya aure ta yagama da cewa da mata ta gari, yayunta kaf aiki suke Kuma manyane batada girman kai.Huum ina ni ina Ita,har sun shiga mota ya fito da sauri yayi gunta,sallama yayi mata juyowa tayi tace...............``` _2 u FUTHA Luv._ *@ut@r h@jiy@*💅🏻 *®NWA®* [11/10, 8:13 PM] ‪+234 809 308 3613‬: 🌹🌹FUTUHATUL🌹🌹 KHAIR🌹🌹 *©Zainab Y Hussain* *Page 36-40* ✍🏻``` Wa alaika salam,murmushi yayi mata,hav a sit,tace masa xama yayi kusa da ita,shuufi ya akhy d'agowa yayi I'm not understand what u want say,OK kenan bakajin larabci?yeah only English,Hausa nd Fullanci I hear ok,amma kayi kama d larabawa kodan kana kula larabawa shine kasatarmana kama,dariya yayi yace inji wa?ai Hausa sunfi kowa kyau ta ina,ku baqaqe kuma noo!ai ko da baqinmu munfi ku kyau haka sukayi ta hira kamar sunsan juna,kallonsa tayi tace xanshiga lecture 12:30 mu keda Ita,but bansan naxo lat shiyasa nake xuwa before time en yayi, so I have to go now,tnq see u next time.Can I have ur number mexakayi da Ita, gaisawa ok,fad'amasa tayi.``` *Komawa yayi suka tafi,yah Abdallah yanzu muna komawa airport xan kaika koh, no barshi nama d'aga tafiyan nan da three days kawai, dariya yayi yace lallai Zainab taci gari.kafin yabar garin soyayya ta qullu tsaka insu dan har gidansu yaje kuma ya gaisa da iyayenta,sunmasa tarba ta girma,haka ya tawo 9ja badan yaso ba,kamar ya xauna.bayan saukarsa hutawa yayi yaje yasami Aunty Meenah yace Aunty yaudai nasami budurwa murna tafara wow my broth a ina ltake, wacce lucky d'in ce tasami xuciyan qanina,dariya kawai yayi yace Aunty a Libya take,Libya! Yanzu karasa wadda xaka d'akko duk 'yammatan garin nan har saikaje Libya, Aunty plx bansan irin haka daga farawa da kushewa,ni Ita nake so,Kuma itama tana sona,indai bahaka Wllh I can't mary any gal,haka yasakai xai fita da qyar ta rarrasheshi ya dawo,amma still be koma normal ba,yanzu ya kake so ayi Good inason kifad'awa Phapa aje garin ayomun tambaya,haka akayi basu sha wahalan komai ba,dan sunada kyakyawar alaqa tsakaninsu da hausawa,biki kawai akasa,komai da lokacinsa gashi yanzu yaxama tarihi dan kwanan Zainab uku kenan gidan Abadall tattala juna sukewa Kansu,yana bata kulawa dai dai shi,'yan uwansahaka take kulasu duk da Ba Hausa bakinta amma yanayi da hannu kota tsuguna yadda taga friend nata na school nayi.* ``` Ku hangomun Chuchu lokacin da Abbanta yaxomata da maganar auren kuka tasa yanxu baba babu yadda xakayi gaskiya kace a'a wama xaya aura?Huum shegen yaro 'Yar gidan vice President na Libya ya d'akko Kuma kinsan halin ubansa baxai yadda ba,aikece Allah ya qara saidanace xanmasa magana kikace a'a gashi nan,kuka kawai take,uwarta kuma tace Chuchu Indai inada rai Wllh Sai kin auri Abdallah ko xanyi yawo tsirara,xanyi maganin su bakiga har wani d'aga kai shegiyar Meenah keyiba,Har uwar tasu xanyi magani,bara na nutsu riba biyu ma,'yar kallon uwar tayi tace wacce irin riba biyu?hhhh baxaki ganeba Yanzu mubari komai ya lafa,before muyi komai itama kanta Yarinyar aikinsan uwar kud'i garesu balantana larabawa kinga gold din nata har kud'in shima ai riba ne agunmu,kisha kuruminki.``` *Kwanci tashi Yau watan aurensu shida Abdallah mara magana yanzu kuwa ya iyata,kulawa Ba wadda bayayiwa Zainab, yayunta sunxo haka suka tafi suna farincikin ganin 'Yar uwarsu cikin kwanciyar hankali,Ga rabo ansamu shiyasa yanzu kulawar yanzu tafi ta da,'yan uwan mijinta suna aonta ,Aunty Meenah duk inda xata da Ita suke xuwa indai dangin Sune, Gidan qanin Abbane kawai bata samun fuska koda yakaita shi yasa itama yanxu ko yace yaje bata xuwa,tanada kirki Amma bata jurar iskanci ko Waye shiyasa bata shiga harkar mutane balantana ayi mata ta rama ace batada kirki. Cikinta watansa takwas siyayya harda ta hauka sukayi basuda burin Allah ya nunamusu ranar fitowar Baby.* *@ut@r h@jiy@* ®NWA® 2 u FUTHA luv [11/10, 8:13 PM] ‪+234 809 308 3613‬: 🌹💅🏻FUTUHATUL🌹💅🏻 KHAIR🌹💅🏻 *©zainab Y Hussain* *page 41-45* *Mamanta taso taxo gida wanka Abdallah yanuna baisbakuka ta haqura.yau tana xaune daga Ita Sai vest Sai xani wanda shima daga kaga yadda aka d'aura kasan koyo ake,vest d'in Kuma iya kan cikintane fruit take sha din favourite dintane koda tana gida,remote ne a hannunta tana sanja chamel, sallama taji,tanada daga kwance ya miqe xaune Wa alaika salam,sannun ku bissmillah Ku xauna haka suka xauna,Jegal kina ina da sauri wata yarinya tafito xama tai kusa da Ita,na'am aunty baqi ne sukaxo kawo musu drinks mana,tom,ke! dawo suwaye baqi mu ai minfi qarfin baqi saidai 'yan gida,qannensane ko bakiga kama ba,ko hasken idon naki bai washeba,ko xakice baki ganemuba,samun gurine anxo qasar mu amma anson afimu ikoh da ita ,dariya ta sau musu, au ashe ba baqine ba 'yan gida ne Sannu bansan kunada kamasho acikin gidan ba,ai da kuna xuwa ciki xaku shiga, kul niba irin useless mutane bane da xa'a raina ban tolerating noincess dama har yanxu akwai daqiqai irinku,gidan miji basuyi maka sai 'ya'yan qanin uban miji wanda uba d'aya suka had'a ba uwa ba ,to kul bansan hauka,oya kuficemun agida,kut Aunty Chuchu kika bari tana xafin babanmu wallahi sai mun xaneki kuna d'ora hannun Ku kwanan cell farillah akanku.* ```Haka suka fita gwiwa a sace tundaga wannan lokacin suke Neman hanyar da kota halin qaqa Sai Chuchu tashiga gidan kuma tarabata da mijin datake taqama dashi.lallashinta yayi yace kiyi hakuri Rayuwana Kinsan Idan hauka yakama mutum,Yaya nice mahaukaciyar au baku fita kun barmin gida Ba,haka suka fice.``` *Yau tun safe take jin badad'i jikinta haka take daurewa har Maigidan ya shirya, dan tafiya xaiyi Kwana d'aya kawai xaiyi, Kuma ix important meeting yakeda shiyasa bata nunamasa komai ba,amma duk da haka sai daya tambayeta any problem nothing tace masa Har gate tarakashi,sunana juna bye bye. Ai kamar jirajira haihuwar take ya fita gaba d'aya taxo one time gashi jegal bata nan Ga naxata iya fita ta d'akko wayantaba,sallama tajiyo daga parlour jin ba'a amsaba yasa yadhiga d'akin Chuchu ce ganin halin datake ciki yasa tayi tafi tace Zainab yanxu yaxakiyi ga mijin naki baya nan sai maqiyyarki kina ganin xan taimaka miki eh tace hhh,Amma kinyi kuskure harta juya komai ta tuna da sauri taxo kusa d Ita kanta tayi tasata a motor da gudu tafita a gidan.shi kuma wayarta yaketa kira shiru yana son fad'a mata xaishiga jirgi,haka ya tafi bai samuta answer ba,qofar wani gida ta kaita Waya ta d'akko hello mama anan tafad'amata komai,Chuchu amma ke wawiyace ai dahaka xamu sami damar komai akan su maxa JUYA ki kaita asibiti, gani nan xuwa haka suka tafi kusanrabin 'yan gidan,basu dad'e da shigaba akace ta sauka state suka tmby me aka Haifa ? baby girl ne,hamdala sukayi da dariya,saida aka gamamata komai sannan akayiwa gidansu Abdallah Waya aka fad'a masu.* ```Chuchu da kanta tabugamasa waya amma no respond,kamar tayi kuka Lokaci Lokaci tana bigawa,'yan gidansu sunxo aunty Meenah murna take balantana dataji baby girl,Itace tace yanaganku da yawa Kuma ina Abdallah, Chuchu ce tace baya nan, nashiga gidan naganta tana kuka Har Xan fito dan kar ace nayimata wani abu,tunda aunty Meenah mu yanxu kun maidamu kamar Ba qannenku ba,tausayi yasa naji koda xaku yankani saina kaga asibiti,kanta ta Shafa tace haba Chuchu yammatan Abbanta Waye yace bansanku halinkune dai banso amma let pass be pass,'yan qannena,Allah yabaku miji musha biki ko ansamune ake rowar nunawa big aunty shi,haka sukayi ta wasa da dariya ,Har aka sallamesu.``` *2 U FUTHA Luv* ```@ut@r h@jiy@```💅🏻 *®NWA®* 🌹🌹FUTUHATUL🌹🌹 KHAIR🌹🌹 *®NWA* *©Zainab Y Hussain* Page 46-50 Gida suka kaita d'akin ta suka gyara,tea tace aka mata ahaka sukayi xaman awa biyu duk da haka number Abdallah take try amma bata samuba Wajan axahar wad'anda suke Sallah cikin su suka tashi dama Chuchu oga CE wajan wasa da Sallah yanxunma tana zaune Aunty Meenah ce tace 'yammata atashi ayi Sallah kobakiyine naga kowa ya tashi Dariya tayi tace big Aunty pastor ne yaxo, a'a to sha zamanki Ummi ce tace aunty Chuchu yaushe kika gam..... Dallah yiwa mutane shiru munafuka uwar gulma dama biyu ya had'emata Ga rashin samun wayar Abdallah ga aunty Meena tayi tsaye akan komai takasa samun new information akan Zainab shiyasa take yiwa Ummi masifa Wayar ta d'auka dialing tayi unexpected taji tana ringing wani dad'i taji axuciyarta amma harta kusan hanging bai picking ba,saidaga can ya d'auka salam abinda yace kenan,ina yini Yaya"lafiya ,ya kk? normal yace,albishirinka yaya cike da zaquwa yace goro Chuchu yanzu na sauka ko hotel ban shigaba fitowa ta kenan daga gurin screening so kiyi hanging up nata I 'll cll u back zai katse tace,Yaya don't hang it,Aunty zee ta haihu,kamar daga sama yaji ,repeat again Aunty ta haihu Idan baka yadda ba ga aunty Meenah ,hello broth Zainab ta sauka Plx Aunty ar u sure "yeah lemme give her,alo baby,hello my xee waikin haihu kafin ta bashi answer baby tafara kuka Daga cikin wayar qara yasaki kamar wani Yaro, Alhamdulillah Allah yaraya baby,is she girl? Yes amma kama dani take koh?a'a da Mamanta take kama,anya kuwa kura da shan bugu gardi da d'auke kaya tashi tayi tsam,bed room tayi,me kace wane gardin wace kurar? Hhh nine kura ke Kuma gardi,tunda ninayi kayana ko xaki iya haifarta ke kad'ai,naji amma Waya d'auki cikin, ke kuma waya sa irin da aka haifa ,huum kai bakajin kunyar magana yanzu Ashafan kan baby dai ace Abban ta na gaidata,xataji fitowa tayi Chuchu tabawa phone d'in " Yaya"na'am Ina gift d'ina? me kike so Yau inacikeda murna wallahi qanwata da ban tawo ba baxan zoba,amma nan da ten hours Ku jirani xanyi qoqari ayi komai yau,dana meeting ne akan wad'anda akesan sufito election, tom Allah ya saukeka lafiya Ameen yace Karfe tara na dare a sokoto tayimasa yayi murnar baby,sosai Family nata sunzo suncika gida abinka da 'yar masu gari kusan rabin hotel d'in dake garin sokoto saida suka cika 'Yan gidansu Chuchu dasu ake komai, kaf sun mamaye dangin Zainab . Dedicated to FUTHA Luv By @ut@r h@jiy@💅🏻 [11/10, 8:13 PM] ‪+234 809 308 3613‬: 🌹💅🏻FUTUHATUL🌹💅🏻 KHAIR🌹💅🏻 *®NWA* *©Zainab Y Hussain* Page51-55 ✍🏻Ranar suna yarunya taci sunan BILKISU sunan kakarsuce ,mai jego tafito sosai kowa sai san barka angon k'arni shima ba'abarshi abayaba,kwalliya yaci akad'inga pictures dashi,Abba da safe yazo yaga jikarsa,dayake yatafi umrah, so baisamu xuwaba Sai ran suna,trolley guda yacikamata balantana xataji sunan Mamansu aka saka sun masa kara shiyasa shima yayiwa baby siyayya, "sark'an gold ita kanta ta 150k ya siyawa babyn itakuma surukar tasa,Bangles ne da zobe 'yan ubansu English gold ya bata,zokaga bakin ciki gurin su Chuchu dan har kwalla saidatayi,dayake agabansu yazo,Mamana ma kyauta tayimata ta wani super market nata,Aunty Meenah uwar 'ya itama gold ta bata,'yan uwa kowa yayi abin arzik'i daga part d'in Abdallah harna Zainab. Alhamdulillah anyi suna lafiya angama lafiya komai da 'yan gidan su Chuchu akai family'n Zainab duk sunsnsu har murna suke kowa nasan 'yarsu shiyasa komai xasuyi ko su fad'a agabansu akeyi har lokacin da suka tafi,Chuchu itane oga wajan rakasu airport har qawa tayi wata Mamu kyakyawar gaske,haka danginta suka tafi sunamasu cike da kewar 'yarsu. Chuchu 'ya kullum tana hannunta, kusan tarewa tayi agidan,ganin yadda takewa baby yasa suka yadda makamin qin kula su,shida kansa yanzu yake kulata ayita wasa da dariya. Bayan wata shida Yanxu kusan rabin sirrin Zainab Chuchu tasani dan yanxu bata mata shamaki akan komai.sukuma ayanxu ne sukeda lokacin aiwatar da kudurinsu akan Abdallah bawai son Allah takemasa Ba,a'a kud'in sa take so,da kuma tara bashi da Mamansa,dan uwarta tacemata tunda aka aurota Mamansu Abdallah ta tsaneta,kuma itane jigon da dangin mahaifinsu basa k'aunarta,tak'ara da cewa babansa kuma lokacin da Abban ki bashida kud'i ko garin kwakwi baya bamu,sai yayi sadaka agaban Babanki amma baxai bashi ba Da wannan tayi alkawarin saita rabashi da dukiyar kuma tasa baxaiji maganar kowa ba,sai tata Baby ta girma kuma tasan Chuchu dan daga ta ganta xata fara mika hannu. Mama ya kamata asan abinyi Lokaci na k'ara tafiya dame ya kamata nafara,Kinsan yanzu Hajiyarsa tana sona balantana dataga yanzu inason kowa kuma inasa kaya masu kyau Riga da zani,yauwa to yanxu gidanta xaki fara xuwa kina d'an tayata aiki,kuna hira wani lokacin ma kwana xakiyi kinga Idan abin sha ko ci,malam ya bayar kinga baxamuyi wahalar xubawa ba Amma Idan baki koyi xuwa ba abin xaiyi wahala, uwar xamufara karkatar da hankalinta da ita shegiya Meena d'in Good haka nake sonki ahaka kamar baxakiyi tunani irin haka ba,yo ance miki ni tawasace Kashewa suke ,ahaka tafara aiwatar da qidirunta,Kuma yaci dan yanxu hajiya Ita da Aunty Meenah sunsake dasu sosai wani lokacin Ita hajiya ce take cewa ikon Allah ashe rashin xama da mutum ne yasa kake ganin kamar bashida kirki Yanxu komai yaxomusu da sauqi,Abdallah kansa yanzu har Waya yakewa Chuchu. Dedicated to FUTHA Luv By @ut@r h@jiy@ [11/10, 8:13 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [23/09 1:32 pm] @ut@r h@jiy@💅🏻✍🏻🌹🍇💖🌷: [23/09 12:18 pm] @ut@r h@jiy@💅🏻✍🏻: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussain* *In dedicated to Bilkisu sidibe, Futha Luv* _Page 56-57_ Haka rayuwa ta ciga da tafiya, Chuchu taxama 'yar gida, yanzu batada shamaki acikin gida, magani yafara aiki duk da har yanxu ko d'aya bai canja mata ba, amma ga dai yanda ada yakewa Chuchu rashin sakin fuska, yanzu ba haka abin yake ba Dan, hira sosai yake janta, dashi, kuma abinci ma tare akeci da ita yanxu Hajiya yanxu zumunci sosai wanda ba'ayi da ba, shi su ke yanxu Mama, ya kamata fa gaskiya, yanxu salo ya canja saboda ni dai hak'urina ya k'are, shegiyar Zainab d'in can kamar k'aramata kyau ake Yana kula ni dai, amma fa Zainab itace star, saboda kullum kamar baby take koma wa, gata da shashashar 'yarta, FUTUHATUL KHAIR, kullum bashida magana saita baby futha Hakane Chuchu, nima yanzu nake tunanin haka, dama boka yabamu sa'a wannan watan, yanxu ina layar da aka baki?, tana cikin kayana, yauwa saiki sami wani kuje mak'abarta kisami tsohon kabari wanda ya bud'e ki cilla ta da baya Kina cillawa kada ki juya, sai ki tawo da gudu, Mama aike zaki mak'abarta bani ba Kinga shashasha keda xa'ayi wa aikin aike yakamata kiyi aikin da kanki, bani ba, hauka nake zani mak'abarta Kedai kije, Mama gaskiya ban iyawa, shiga mak'abarta ai sai maxa, eh lallai bakison auren Abdallah da kinaso kuwa da babu abinda baxakiyi ba Abba ne, dayake shigo wa yace, kyaleta Hajiya, ita zatayiwa kanta, da mu, dan idan ta samu ai kamar mune To Abba, kazo muje, itafa wai naje ni kad'ai, a'a haka nace kisamu wani kuje To yanxu dai, abari sai gobe, aje Dan kinga tsamirmiri yace, indai har an jefa wannan layar, bashida katab'us sai abinda mukace Kuma idan an tabbatar an jefa, shine zamusa wancan audugar mai sunan sa Dana 'yan gidansu, acikin mai Abba ne yace to shi kuma wannan amfani me gareshi? Hahaha, ai kusan shine babban aikin, dan indai babu wannan to bazamu samu kan 'yan uwan saba Yanxu idan aka saka audiga cikin mai, yaxatayi? fad'a mun da kanka Lallai kin cika shu'umar uwa, hala aikin kika yi mun, tabbas idan aka saka audiga cikin mai, batada katab'us lakwam zatayi, sai yanda aka juyata To haka mukeson muyi musu, kud'i da komai nasa saiya dawo hannun mu [23/09 1:32 pm] @ut@r h@jiy@💅🏻✍🏻: Dariya sukayi du kkansu Allah sarki baiwar Allah ita lokacin da suke mata wannan d'anyan aikin, ita lokacin ne take tsaka da addu'ar Allah ya kiyaye ta ya kiyaye 'yarta Saboda wani irin mafarki datake akan ta da Abdul d'inta, akan wai wata tanason rabasu, hannayensu kullum a had'e suke, amma kwanan nan saitake ganin kamar suna nesa da juna Ayaune tunsafe suka tashi, Abba ne akan gaba, wajan zuwa wajan cilla laya Har sun shiga mota, sai aka yiwa Abba K'anin Mama ne, kamar bazai d'auka ba, sai dai yayi picking "Hello" "Hello ya gida, lafiya lou, Abbane yace yanaji muryarka kamar da damuwa? Eh wllh, Hajiya babbace Allah yayi mata rasuwa, me kace? Abinda kaji nace, ai kuwa sai hawaye Abba, saboda surukar sace Babar mama CE, mutuniyar arxik'i ba irin 'yar ta Chuchu ce tace, Abba me ya faru? naga kama kuka, menene Hajiya Babba itace ta rasu, yanxu Inalillahi" mun shiga uku Abba juya, haka suka juya gida, saboda suna son kakarsu sosai Ai suna shiga da gudu tafad'a jikin Mama, wayyo Hajiya babba ta mutu mun shiga uku Wace Hajiyan? Hajiya fa, ai kan kace me gida ya rikice haka, suka fara had'a kayan su dan zuwa gidan mutuwar Jirgi suka shiga, daga Nigeria🇳🇬 zuwa Burkina peso, dan mama ba 'yar k'asa bace *Wnn shine yayi silar rugujewar aikin su* By @ut@r h@jiy@💉🌹 [11/10, 8:13 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [23/09 2:19 pm] @ut@r h@jiy@💅🏻✍🏻🌹🍇💖🌷: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussain* *Dedicated to Bilkisu Sidibe Futha Luv* _Page 58-60_ Haka suka tarkata suka tafi, ansha kukan mutuwar kaka, mama kuma uwace gunta Abba satinsa d'aya ya juyo saboda anyi sadakar bakwai tareda su Zainab da Abdallah suma sunjewa Mama ta'axiyya, Chuchu dai bata nan lokacin da sukaje, tana wajan wani saurayi wanda suka had'u akasuwa lokacin da sukaje cefane Aranar suka je kuma suka juyo, tareda Abba K'aidar garin da suke, indai akayi mutuwa to 'ya'yan wadda ta mutu da jikokin ta, agidan zasu zauna har tsawan shekara d'aya, daga nan kuma sai ayi rabon gado Haka ta kasance suna can, axaune, maimakon suyi sanyi ganin yau suna tare da kakarsu gashi an wayi gari ba ita Amma ina, sai suka bud'e sabon shafi na watsewa, kowa haka tayi saurayi, babu laifi kyawawane shiyasa 'ya'yan manyan garin suke d'aukan su Amadadin ita uwa ta tsawatar tayi fad'a sai take ganin kamar wani abin arzik'ine 'ya'yanta basu da bak'in jini, kowa yana son su Kakarsu ta yanke saqa, tunda yanxu fantamawa suke, komai baja baja agidan, dama Mama ita kad'aice 'ya a gurin ta shiyasa batada mai mata fad'a Akwai wani qani ne wajanta, sosai yafara mata fad'a amma bud'ar bakin ta, sai cewa tayi baqin ciki ake, saboda yaranta Allah yabasu samari masuyimusi busha sha Ba yanda ya iya, haka yatafi ya kyalesu Duk da wannan kud'i da gold da Chuchu take samu, Abdul d'in Zainab na manne a zuciyarta Tayi qoqarin tafiya, Nigeria🇳🇬 amma, ba hali daboda tsarin garin *Bayan shekara d'aya* Yanxu sun dawo gida, rayuwa sabuwa kowa ya bud'e Kwanansu goma da dawowa suka shirya sai wajan tsamirmiri, wannan karan babu sa'a, dan Aljanin dayabasu wancen aikin yatafi bauta, kuma baya dawowa sai bayan shekara d'aya da rabi Yanxu boka Allah ya tsine, mai maida mai hankali mara hankali, mai juyar da kwakwalwa, ya zamuyi? Gaskiya sai nan da wata shida saboda alokacin ne zai dawo Haka akayi, dubu d'ari suka ajiye masa saboda xa'ayi yanka, kafin yaxo aljanin shima zai fara aikin Sosai suka koma wa Zainab, amma wannan karan bata sake musu kamar da ba Saboda tafara aiki, a asibitin AKTH sosai, tasamu karb'uwa gata kwararriya akan sanin makamar mata To d'an xaman da tayi, a sanjje a hankali tafara gane halayyan mutane Kuma ana bata labarin, ya da qannen miji suke, da yanda 'yammata suke kwacewa mace miji, har cikin gidanta Sosai ta canja, babynta tayi wayo, shekara ta uku tasaba da kowa baran ma, kakarta tunda yanzu sai tafi kwana. biyar a gidan Yarinya kyakyawa, gashi har baya, babu inda tabar Maman ta komai da komai, batada farin jini Ansata makaranta NAGARTA Nur & PRI school, kwakwata yarinyar batajin Hausa sosai, daga larabci, yaran Maman ta sai fullanci yaran Babanta, sai English Duk inda ta shiga sai an sota, batada qiwa, ko d'aya, babanta duk inda yake zuciyarsa naga 'yarsa Yawancin fita da ita yake, wani lokacin har cewa Zainab take, yafi sonta akan ta yanxu, saidai yace ai son kine ya shafeta Wata irin d'anyar qauna da so yakewa matarsa da 'yarsa Auntynsa kusan duk sati sai an kaimata futha, Alhaji nasu ma, yarinya ina balarabiyar gidan shiru ba'a kataba Ko Abu wani yake so daga waje, indai ya had'a da FUTHA to kalas anmasa angama [23/09 2:29 pm] @ut@r h@jiy@💅🏻✍🏻🌹🍇💖🌷: Ranaku na tafiya, sati na wucewa watanni na zuwa, gashi yau anci wata shida, kuma ayau suka koma gidan malam Sa'a tafi laya, dan kuwa duk abinda suke nema sun samu, kuma aranar aka cilla laya, kuma aka saka audugar cikin mai Allah sarki, baiwar Allah yanxu tana rayuwa cikin dad'i cikin Salama da kwanciyar hankali, amma nan da lokaci kad'an zata shiga gararin rayuwa Tsafi gaskiyar mai shi, dan gashi yau Abdul tarairayar dayakewa matarsa babu, saidai 'yarsa Jiya ke gaba d'aya Chuchu itace aransa, Zainab ita bata ka komai ba, amma dai bataji dad'i ba Hajiya kanta, 'yar wayar datake mata, gashi kwana biyu babu ita, daga ita har Aunty Meena Addu'a ita tasaka agaba, duk da Abdul canjawarsa kad'ance wajanta, saboda k'arfin addu'arsa, su Hajiya ne dai abin sai a hankali Chuchu tadena zuwa gidan, saboda maganar boka yace kada tabari su had'u da matarsa har sai bayan anyi aure shiyasa kwatakwata tadena mata koda 'yar wayar datake mata By @ut@r h@jiy@ 💅🏻✍🏻🌹🍇💖🌷 [11/10, 8:13 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [23/09 6:33 pm] @ut@r h@jiy@💅🏻✍🏻🌹🍇💖🌷: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussain* *Dedicated to Bilkisu sidibe (Futha Luv)* *Page 61-62* Haka tafiya tai ta tafiya, Abdul yaune yaje gida wajan Chuchu, hira suke ta yi, tanata tambayar sa ina Futha, dariya yai yace 'yammata tana gida, Mamanta yau ta riqeta da wai saita biyoni Me yasa baka tawo da itaba? A'a haka kawai, yanxuma kinga nasan tana can tana kuka, bara na tafi Tafiya kuma, bayan ko lemo baka sha ba, no I'm OK, next time xansha Rafar d'ari biyar ya ajiyemata, ya tafi Tsalle tayi, tace Mama lallai, kinga 50k one time, dole ak'ara shiri, haka dai daga 'yar har uwar sukayita kwakyaruwarsu Amma Chuchu yakamata dai yazo ayi magana, dan ba zuwan ba, yazo ayi, kidai yi masa magana, tom Mama nima abinda nace kenan, matsala ta d'aya, har yanxu ban kamashi yadda nake so ba, shegiyar 'yarsa ma ni ita tafi tsayamin arai Abban Futha, na'am Ummin Futha, ya dai, meya ke damunka?, naga kwana biyu totally ka canja, kafiya zama kai d'aya, ko wani abu ne? Babu komai, Matar albarka, wallahi kwana biyu dai sai a slow, kansa tafara shafawa, tace kana sakaci da addu'a koh? Kwantowa yayi jikinta, yace wallahi banyin sakaci, inayi sosai, saidai dole akwai lokacin da zaizo kana wani abu, shi kenan kadai dage Abba ne, yau yatafi gidan Alhaji, har cikin parlour ya shiga, sosai Hajiya ta fito suka gaisa, tanata washe baki itada Alhajin, ah to an rubucesu Magana ce dama nace bara nazo naji ko kasani, dan kada ace nayi rashin kirki, ko naqi na gida nabawa na waje Alhaji ne yace banganeba, yauwa Abdallah naka, yana zuwa wajan Chuchu naganshi kuma namasa magana yace zaiyimaka magana, to gaskiya kwana biyu da ya wuce, wani Yaro yazo intak'aicemaka jiya ubansa ma har guna yazo Bayan mun gaisa yake nunan magana ce kan 'yar waje na d'an sa yana so, shine nace gaskiya sainayi shawara Yanxu ya ake ciki, yana so, ko kuwa nayiwa wancen magana? Hajiya ce tace, a'a ya xa'ayi haka, gida bata qoshi ba, aiba'abawa dawa ba, bansan da maganar ba, amma indai yana so ai farin cikin mune, Chuchu dama 'yar gidan sace,(kaji aikin asiri) Kiran sa akayi awaya, Alhaji yace yazo yanxu yana son ganinka, tom gani nan Baba Haka ya tafi, maganar akayi, nan da nan ya amince yace ai dama yanaso yayima Alhaji magana, (lokacin da Abba zaizo saida akaje gidan boka yanada sa'a) Ai Abba baibar gidan ba, sai da aka saka biki, wata biyu Tunda akace magana taxama babba, shi kenan yake jinsa wani iri, hakalinsa a tashe, shi yarasa meyasa ya amsa Tun Zainab na tambayar sa yana mata k'arya, haryazo ya fad'a mata komai, sosai tashiga shock no wonder shiyasa Chuchu tadena zuwa Nuna masa tayi ba, komai kunsan larabawa da kishi, amma Zainab ko a fuska, saima rarrashinsa tayi ganin yana neman sa damuwa Biki kuma sai matsowa yake, Maman Futha batasa komai arantaba, tabarwa Allah komai, tunda batada dangi ko d'aya a Nigeria🇳🇬 sai abokanan arziqi, dasuka zama tamkar 'yan uwanta Sai kuma Aunty Maijidda data zamar mata uwa, sai kuma abokanan aikinta, irinsu Nafeesa Anker, Afreen, Jidda ja'o data zamar mata tamkar k'anwa, batada abin cewa sai San barka sune ke bata shawara, akan komai, kuma da addu'oi da suke bata, Alhamdulillah yanda tazaci komai sai abin ya xomata da sauqi Dan Abdul ko d'aya bai ragamata da abinda yake mata ada ba, danginsa, dai aka shanye dashi ta wani b'angaren, amma wajan kulawa da 'yarsa da ita, basu sami galaba A yau aka d'aura Aure, bayan shagalin da aka d'auki lokaci anayi, Amarya part d'inta daban Anqawata mata shi, da kayan alatu, amma ko kad'an bai kama qafar koda kayan kitchen d'in Xainab ba, kada kumanta itafa 'yar gidan vice President CE ta qasar [23/09 7:38 pm] @ut@r h@jiy@💅🏻✍🏻🌹🍇💖🌷: Libiya, kuma yayunta manyane a manyan ma'aikatu, duk wannan badak'alar da ake, ko d'aya bata tab'a bugawa gida ba, akan wai tanada matsala Ankawo Amarya, kuma kowa a dangi sai murna yake, tunda sunga Hajiyan ta canja hali Haka kowa ya watse aka barta daga ita sai halinta. Ango tun wajan, k'arfe bakwai ya dawo gida, amma ko d'aya baiyi gigin shiga ba'arin kowacce ba, dan baya cikin hankali sa Ita Zainab tana can tunanin yana wajan, Amarya, ita kuma Chuchu tana tunanin yana shashin Zainab Haka kowacce ta kwana da haushin kowacce, saida safe Chuchu ta shigo take cewa uwar gida, kin kanainaye komai, mijin ma ba'a aramin shiba, Zainab cewa tayi banganeba? ai a wajanki ya kwana Ban kwana wajan ko wacce ba, dole ne? Kinga fice kibawa mutane waje, kinyi nasarar aurata amma bazakiyi nasarara samun jikina ba, insha Allah Jikina, kinga ya nuna Zainab natane ita kad'ai, yana gama fad'a ya juya ya koma hanyar dayabiyo Lallai bokanki yabaki sa'a, amma kisani wallahi sai kinzama abin tausayi, dama bason Allah na nuna miki ba, kingaje komai saike d'aya mu xuba ni dake aga mai nasara Haka taqaraci maganarta ta fice, tana fita ita kuma tayi d'akin sa, kusan fad'a sukayi akan hakan amma yace itama idan tagaji dashi to tafita, ba yadda ta iya haka ta daure Haka xaman yayi ta tafiya, wataran dad'i wataran mad'aci, mad'acin daga b'angaren dangin Abdul ne wad'anda ayanxu suka juyamata baya, ko Futha dasuke d'auka yanxu sun daina Dad'in ta dasamun sauqinta mijinta babu abinda ya canja mata, saima k'ara kula da ita Haka aka d'ebi shekara biyu, har yanzu Chuchu bata samu kan Abdul ba, duk yanda tayi, abin yaci tura Lokacin FUTHA nada shekara 6 yarinya kamar ita tayi kanta Muje zuwa dai By @ut@r h@jiy@ [11/10, 8:13 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [24/09 9:23 am] @ut@r h@jiy@💅🏻💦✍🏻🌹🍇💦💖: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussain* *Dedicated to FUTHA LUV* _Page 63-64_ Har a wannan lokacin Allah bai qara bawa Zainab ciki ba, kuma bata saka damuwa arantaba, tasan cewa Allah shine mai komai, yanda yaso haka za'ayi Tunda yabasu FUTHA ma, yaba su abu mai daraja, saboda 'yarta mai nutsuwa ce, duk da qarancin shekarunta Yausu Chuchu an qudiri aniyar cewa kota halin qaqa sai tasamu zuciyar Abdul, koda hakan na nufin zatayi yawo tsirara Dama ai tsirarar kike, tunda da auren ki kike kai, kanki wa miji Wanda bana kiba Haka tunsafe tafice daga gidan, dama ai ba maganar tambaya, tunda ko kallon inda take bayayi Iyayen sa kullum cikin fad'a suke masa, akan ya zab'i bare ya bar 'yar uwarsa, shiyasa yanxu kwata kwata basa shiga shirgin ta, itama data fuskanci haka, bata shiga nasu, sai dai duk qarshen sati zataje ta gaidasu Ada can, yini take agidan, sai dare take tafiya, amma yanzu ko awa biyu bata iyawa *Birnin gwari* shine garin da aka tafi, aka wuce tsaunuka, da bishiyu, sannan aka haura bukkar *Boka Nargas*, wanda idan ka ganshi, kai kace irin tsofin *gorilla* ne saboda bak'i da munu, gashi gajere Haka suka tamfatsa cikin bukkar, yasan da zuwan su, tunda wata qawartace tayimasu hanyarsa, kuma shi bucking akeyi, bawai kaxo da ka ba Suna shiga kafin yace komai, sukaga wani qullin abu cikin bakin wani qaton kifi, sosai suka razana saboda basu tab'a ganin kifi mai girma haka ba Kud'auka yace, angayan komai, basai kun fad'a ba wannan kullin, shi zaki d'auka tareda wan nan kan kifin, kisamu k'aton dutse ki d'oramasa, kinga bakinsa zai rufe, idansa zai rife, kunnansa zai rife, bazaiga kowa ba saike kuma guri da kikasan idan aka ajiye babu mai zuwa balantana ya gani Abu mafi sauqi, ki samu qasan gadonki, ko kid'ora dutsan, ko kisamu turmi na qarfe ki d'ora, tunda babu mai shiga cikin d'akin ki Wannan shawarar uwarta mahaifiya, itane tace haka, dariya yai yace kinyi dai dai, Ku zube Ku tafi, wannan kuma layar ki tabbata kinsata gurin d'umi, inda sanyi bazai shi gaba Ma'anarta, bazai qara kusan tar taba, harsai randa layan sanyi ta ta b'ata Haka suka ajiye masa kud'i, suka fito Basu tsaya komai ba, a hanya, gida suka tawo, sunata sheqa dariya irinta arna *Wannan shine mafari* Zuwansu gida ba jimawa, suka fara aiwatar da qudirunsu, saida suka gama, tas sannan sukaje cikin kitchen, bayan gas cooker suka ajiye layar, amma saida suka cire one tile na gurin saboda sunsan zai iya d'aukan sanyi Abdul yana office operation yagama, yana hutawa, yaji kansa yayi wani irin juyaeay, idansa ma haka, bakinsa yafi komai yimasa nauyi Haka dai ya zauna, jin xaman ba dad'i yasaka shi fara tattara kayansa, zai koma gida Tundaga gate yakejin wani feeling akan Chuchu, ko kallon part d'in Zainab baiyi ba, ya yi part d'in Chuchu Yana shiga tana zaune, akan kujera, tana ganin sa tafara washe baki, zuwa yayi wajan ta, hannunta Yakama yace I'm sorry Chuchu for evrthin na zalunceki, na kuma tauyemiki haqqinki amatsayinki na mata waje na, saboda haka kiyiwa mijinki afuwa Yanxu bashida lokacin kowa sai naki, dana babyna FUTHA Sosai taji dad'in haka Duniya sabuwa, ita kuma jin har anyi isha'i bai dawo ba, yasaka takira shi, lokacin yana tare da Chuchu "Hello" Abban Futha shiru ina katsaya? Wajan matar sa, mai qaunarsa, mai tattalinsa, ya tsaya, ko kinada abin cewa? Babu tace, sosai tayi dauriya, saboda dama tayi mafarki akan haka, bata ce komai ba, saima addu'a datake ciga ba dayi A haka aka d'auki lokaci ko leqe saidai taganshi ya dawo, Futha ce dai, xa'a turo a d'auketa Iyayen sa basu damu da rashin saba, tunda suma basuda bakin magana, an kulle, kud'i kuwa kamar ruwa haka take maidasu wajan tambayar sa Amma duk da wannan samun data yi masa, bata sami jikin saba, dan kuwa ko tab'ashi baya son tayi, haka tayi haquri tunda tana samun masu gidan rana *Bayan shekara biyu* A haka aka shafe wannan lokacin Abdul bai tab'a koda kallon b'arin Xainab ba, komai nasa kacokan yakoma gun ChuchChuchu By @ut@r h@jiy@ [11/10, 8:13 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [24/09 10:51 am] @ut@r h@jiy@💅🏻💦✍🏻🌹🍇💦💖: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussain* *Dedicated to FUTHA Luv* _Page 65-66_ Iyayen sa a wannan lokacin da ita kanta Meena yayarsa, hankali yafara zuwar musu, tunda ayanzu suna d'an hirar sa, kuma har suna yunqurin zuwa wajan sa Chuchu yau bata nan, shiyasa 'yar aikin ta, yau take gyara kitchen harta wuce saita dawo taga wata Leda, lah aunty ko mancewa tayi da ita? D'aukanta tayi, tasa a saman cabinet Lokacin da Abdul ya shigo gidan lokacin yaji babu abinda yake so irin yajishi gashi ga Zainab Haka ya shiga wajan ta, sosai taga abin kamar almara, baiyi wata magana da itaba, illa nuna mata yayi ta taimake shi, bata tsaya Jan ajiba, tunda itama tanada buqatar sa Haka suka farantawa junan su, magana yake son, yimata amma ya kasa, ta lura da hakan shiyasa koda zai fita saidatayi tofi, a ruwa ta bashi qin karb'a yayi saida kyar Inda suka tafi, badan komai sukaje ba, saidan 'yarsa, suna son itama ya mantata, nan da nan aka yimusu aikin, suka dawo Haka xaman ya kasance Indai bata nan to Abdul yini yakeyi tareda Zainab, wani abin mamaki kuma yanxu tsakanin sa da FUTHA sai harara da duka, ko yaya tazo kusa dashi Ita kuma Zainab takasa fad'a a gida, duk da batasaka damuwa ba, amma dai kowa ya ganta saiya CE kin rame sai dai tayi dariya Matsalar FUTHA da babanta, yasa ta yanke shawarar kaita gidan su Abdul Haka akayi maidata gidan tayi, anan ma bata tsira ba, saboda har yanzu akwai ragowar asiri jikinsu Lokacin data fuskanci bata gidan, takanas taje gidansu Abdul dan fad'awa Maman sa, sai ta ganta agidan Gaisawa sukayi, anan ta yini lokacin da zata tafi batayi shawara da kowa ba, ta d'auketa, haka ta maidata wajanta makaranta ma, tadena zuwa, saiya kasance aikin komai itace lokacin tanada shekara 11, amma tasan me Kishiya take ciki Itama tsareta akayi, ko gigin zuwa gurin uwar ta batayi Rabo shine yakai Abdul wajan Zainab, dan yanzu cikine da ita wajan watansa 5 lokacin kuma yafara fitowa, yau ta dawo daga gun aiki tabiya dan ganin FUTHA, amma wayam tambaya tayi, a daqike Hajiya tace ai tana gidan Ku, wajan Chuchu Bata qarasa ba, ta fita da sauri, sai gidan, FUTHA sunanta ta shiga kira, jin ana karanta yasa tafito da gudu muryan Umman ta tajiyo A sukwane ta fito, me kikazo yimun a gida?, 'yata nazo d'auka mitsiyaciya Allah ya kusa tona asirin ki, mai raba mata da miji, d'a da uwar sa Kinsan badan abinda kika yi ba, kebaki isan Abdul ya kalle kiba, Hajiyan sa ma haka, 'yata tafi k'arfinki, ko shine yabaki bai isaba, kiyi d'an kanki Juyawar da zatayi sai ganin ciki tayi, kut ke Zainab iskanci kika koma? cikin waye wannan?, cikin mai gidan ne, ko shima sai ya nemi izininki? shashasha wahalalliya, haka ta janyo hannun 'yarta suka fice Bata tsaya wata wata ba, ma'ajiyar ta, ta duba? wayam, Munay kina ina dan uwarki ina kika ajiyen ledar da kika gani?, lah asama na ajiye mantata kika yi ta fad'a baya, ai jibgarta tafata yi, ganin dai ta cuceta kuma tsayawar b'ata lokaci ne, yasaka tayi maza ta ajiye shi inda yake Abdul koda yadawo, bai qara bi ta kan part d'in Zainab ba, masifa yashata kamar d'anta, hak'uri yafara bata, amma ko kallo bai isheta ba Safiya nayi, aka tafi wajan boka, magani yabata ta tabata ta tsallake, haka akayi kuwa, tana xuwa ba sanya, haka ta xuba maganin Lokacin da take zubawa, babu kowa, haka tagama ta koma part d'inta lokacin ne FUTHA tana ta wasanta da ball suna hira itada Mamanta akan school nasu, wadda tace ta dad'e bata jeba, ball d'in data buga sai tayi hanyar waje, tana zuwa akaci sa'a ta tsalleke maganin da uwarta yakamata ace ta tasalleke, dan cikin jikinta ya zube Amma akasin haka, yasa ta taka Haka ta dawo, uwar tana magana amma bakinta yaqi ya bud'e dan tayi magana, tai tai takasa, kuka sukasaka baki d'ayan su Asibiti ta kaita, akace komai normal, batada zab'in daya wuce addu'a, ita kuma tasaka agaba Kwanaki na tafiya, FUTHA harta saba, da maganar kurame, daga ita har Mamanta, ciki kuma yanata girma abin sa Ganin cikin yana nan, tayi tayi amma bai fita ba, sai tayanke shawarar sace FUTHA, shine ta d'auketa tabawa wani mutum akan ya taimaketa yakai wannan yarinyar wani gari nesa da Sokoto Maqudan kud'i ta bashi, shikuma bai duba k'ank'antar taba, ya sunkuceta sai NIGER, anan ya ajiye ta agarin Duffa Tafi tafi, harta kai Numeiy, anan ne Kaber ya tsinceta ya kaiwa Matarsa MEIMiE ita *A dawo labari* By @ut@r h@jiy@ [11/10, 8:13 PM] ‪+234 809 308 3613‬: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussain* *Dedicated to FUTHA LUV* _page 67-68_ *Cigaban Labari* Haka itada wannan yaran sukayi ta tafiya, har sukakai inda Mama Anker take sana'ar saida abinci cikin kasuwar sokoto A nan yar bukkarta take, wajena babba, dan harda kujeru da tables a wajan, saiya kasance kamar wani k'aramin Hotel Anan take kwana, itada yaranta, ma'ana masu yimata aiki, tanada kirki a wajan bawa mutum hakkinsa indai kana k'arakashinta zakasha masifa, amma kuma batada bak'in ciki ko tauyewa yaro hakkinsa, itane da kanta take sayamusu bankin k'asa, indai antashi tabasu sallama bazata bari mutum ya kashe ba, zata sashi yasaka cikin bankin Takance, kwad'ayi shike kawo yunwa, kuma babu yunwa cikin Ku Mama Anker dai kowa yasanta, tanada nasibi cikin harkarta, kuma dai dai batada tsada A haka suka k'ara sa, cikin kasuwar Cikin shagon nata suka shiga, yana zuwa kowa yayo Kansu, Kabeeru ina kaje anata nemanka, munzata ka mutu? Shafa jikinsa 'yan uwansa suke Haka dai suka k'arasa ciki, suka zauna, labarin komai yabasu, da labarin itama yanda akayi suka kasance tare Sosai kowa wajan ya tausayamata, jin wanda suke tare ya mutu, ko kuma yana nan itad'ince data b'ata bai ganta ba, kuma gashi bata san garin da zasu ba, wata sabuwa dasukaji bata magana Haka dai aka gama jajantawa, har Mama Anker duk jarabarta saida ta zubar mata da hawaye Kama hannunta tayi, tace zaki zauna a wajena?, kai ta kad'a, yauwa kinga ba wani abu zakiringa yi ba, gyaran d'akina zakimun, idan kika gyara sai kiyi zaman ki aciki, kinga kasuwa ce nan, ta maza bata mata ba Kai ta kad'a mata, d'akin suka shiga, katifa ce, da kujera guda biyu, ga carpet da labulaye mai kyau mai kyau D'aki guda ne, sai band'aki aciki, kan kujera ta zauna, a'a 'yata zauna akan gado, kafin haka ma, tashi kiyi wanka, tunda magari ba tayi sai kiyi sallah Kici abinci sai, saiki kwanta, kisaki jiki dani, kamar uwa nake wajan ki, indai kinbi yanda kike so, kuma insha Allah muna tare zakiga 'yan uwanki Ki kama kanki, ki rik'e mutuncinki, nidai ina k'ara fad'a miki nan kasuwa ce, duk da ni maza nake sawa aiki, kuma da inada wani gidan wallahi da can zan kaiki Amma bandashi, banason munafurci, kuma banason fad'a, ki rik'e darajarki ta d'iya mace Mama Anker, anyi magana a hankali batare da masifa ba, lallai FUTHA taciri tuta, wajan Mama masifa Zaman ta wajan Mama Anker, zamane na kwanciyar hankali, ci sha komai tanai mata dai dai gwargwado, suttura kanta saida tayimata kala biyar Daga dare zuwa Safiya take walwala, amma daga ance mutane sunfara fitowa, zata koma ciki, kallo take zamanyi, tunda solar ce a wajan Mama bata yarda, da ko ragowar ma aikatanta ne, suna yiwa FUTHA magana ba Kuma tundaga ranar da FUTHA tazo wajanta, ta harantawa mazan shiga d'akinta Tafi tafi FUTHA ta d'auki kimanin wata uku, wajanta, batare da ta fuskanci wata matsala daga kowa ba, kuma tana kiyaye maganar mama Anker, shiyasa ba'a tab'a jin kansu ba Amma sautari zata jiyo masifar ta, daga waje, koda customer, koda yaranta Ganin hankali da nutsuwa irinta FUTHA, yasaka mama nemomata cigaban makaranta, tunda takardunta acikin jakar hannunta ta zubo, lokacin dazasu tawo, kuma koda accident yazo, jakar na hannunta Shiyasa dataga takardunta, bataji kyiwar kaita makaranta ba GGC Sokoto nan ta kaita, alhamdulillah tafara zuwa asa'a, tunda dama tanajin komai, mayarwa ne bata iyawa ~@ut@r h@jiy@~ [11/10, 8:14 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [28/09 7:06 pm] African girl 🇳🇬: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussain* *Dedicated to FUTHA Luv* Page 69-70 Haka rayuwarta tayi ta tafiya, har takai SS2 lokacin tazama budurwa, wani irin sirrin kyau, takeda shi, bata kula kowa tunda tasan ita d'in ba wata bace, face 'yar aikin maisaida abinci a kasuwa Mama akullum shinkafa da Miya, sai roman kansa, da wainar shinkafa kwano goma take dafawa, kuma insha Allah kafin dare ta k'are Yau Mama antambayi lafiyarta, ko d'aga kanta bata iyawa, sai rawar sanyi, ahaka kaberu yazo ya ganta, Asibiti a kasamo mota aka kaita FUTHA ita ta zauna, ganin har lokacin da mama ke d'ora ke abinci yakusa, basu dawo ba, yasaka tafito da kanta, hijab tasaka har k'asa, tafara aikin had'a murhu, tana gamawa shinkafa bata san kwano nawa ake dafawa ba Haka tahad'a murhu biyu, shinkafa kwano bakwai bakwai haka ta d'ora, kafin wani lokaci har sunyi, sammuy a hankali itada Musa sukayi parboiled nata, 20 minute suka bata, sannan suka fara kwashewa Tukunyar bata kama ba, haka suka maida ruwan, taliya, nan ma, mama nadafa kwali d'aya, su kuma suka dafa kwali da rabi, Omar shine mai soya waina , kuma dama anrigada anyi markad'enta, da miyar, shiyasa aikin yayi musu sauk'i, kafin 1pm har sun gama Wanke wanke, sukai, tunda sauran yaran taredasu aka tafi Asibitin, haka suka gama komai, sannan suka fara saka cokula kan table d'in Wanka tashiga tayi, doguwan riga tasa, sannan ra zauna kan kujerar da mama ke zama, dayake Musa duk yad'an nuna mata yadda zatayi hakan yasa tafara zubawa mutane masu siya Lokaci kad'an sai yazama abinci kamar rububinsa ake, wad'an da basa siya, saigasu, daga wainar har shinkafa kafin la'asar sai kwano Ganin irin yadda abincin yayi saurin k'arewa da wuri sai kawai tak'ara d'ora wata, itama tanayi ta siyar duka Dayake ansan halin mama da masifa, babu wanda ya tsaya wani maganar banza, amma kowa saiya tafi da santin kyau na FUTHA, ga kuma abincin kowa yaji testing nasa yayi dad'i Wajan 6 idan kazo wajan bazaka ce, anyi wani abu ba, yanda suka gyara wajan, suka kayi k'alk'al dashi, komai suka mai dashi mmazauninsa Kud'i tacira yabawa, Musa tace yasiyo sub'o, kai aiba'a lemo, ko ita tace ayi?, kai ta kad'a masa, alamar a'a, tanason gwadawa ko za'a siya, haka aka siyo kwano biyu, suger rabin kwano, sai flavour, da sweetener dasu tiara, komai dai haka ta rubuta masa yaje yasiyo kuwa. Motar taxi, ita ta ajiye su mama Anker, dakanta take tafiya, kuma kamar ba mara lafiya ba,sab'anin da safe da idan kaganta, bazakace zata k'ara koda second bane D'akin suka shiga, itada kabeeru, FUTHA da sauri ta miqe ta tareta, kan gado ta ajiye ta, sannan tafara jeramata sannu, amsawa take, ruwan zafi ta kaimata toilet tace Mama dazakiyi wanka zakiji dad'i? Kai ta kad'a alamar eh Haka ta shiga, tana fitowa ga flask na ruwan zafi da wainar shinkafa a jiye, bata tsaya tambayar Ina aka sami wainar ba, shi tayi ba miya tareda ruwan Lipton, gyatsa tayi, sannan tasha magani ta kashin gid'e Sallama su kabeeru sukaiwa FUTHA, suma tabasu abincin su, kowa Yakama gaban sa Wajan k'arfe 4 ta tashi, dayake ta rigada ta had'a komai, k'ulli da zuba kayan k'amshi sune suka rage, haka ta zauna ita d'aya tafara k"ulli a leda, ahaka harta gama, lokacin har anyi assalatu haka dai ta daure tagama Cool dream, ta Mama wadda take saida qanqara, ita ta bud'e tazuba a k'asa sannan ta zuba wasu cikin cooler, tana gamawa adaren ta wanke komai, bata koma ba saidatayi alwala tana cikin nafeela mama ta fito Itama alwala tayi, lokacin ana tada iqama, haka suka bi liman, ana idarwa, harzata koma bacci, saitayi tunanin bara tayiwa mama bayani akan abincin jiya, gani tayi tafita, kuma itama bacci takeji sosai, shiyasa ta kyaleta, tace koda safe ta gayamata, haka FUTHA ta koma baccin ta Mama kuma, d'an kayan tafara had'a wa, kafin safiya Tunda ta kwanta, bata farka, sai da wani wawan kira da taji Mama tayi mata Ke, kina ina, alokacin buhari, da shinkafa ke tsada, ke ko garine shima yazama kud'i yanzu, balantana shinkafa, ina aka kaimun shinkafa, kwano goma sha hud'u taliya cartan biyu, nifa gadai markad'ena nagani, wato saboda banda lafiya,kina zatan mutuwa zanyi shine kika had'a baki da wani a cuceni, aka d'ibi shinkafa ta aka siyar, to wallahi afitomin da ita, kuma ki tabbata kin b'acemun da gani Saidata bari takai aya, sannan ta janyo hannunta, Musa yana wajan shima haka ta kira shi, littafi ta d'akko tanuna mata Sosai Mama zatayi masifa, Musa yace mama abinda kike tunani wallahi bashi bane, amma ki karanta kafin kici gaba, da yanke hukuncin D'ai d'ai da d'ai d'ai, tabi tana karantawa, bata gama ba, ta d'akko mata, damin kud'i, kafin kace me sai ga mama na washe baki, balantana data fara irga kud'i, ai sai murnar tafi haka Musa shiyayi mata bayanin komai, aikuwa sai rawa, abinda ya nunku akud'in kashi uku bisa ribar da akeci da Kuma gashi ta nuna mata lemon datayi, sosai taji dad'in sa, lokacin data sha, saiga mama nashima FUTHA albarka A tak'aice dai, mama saidata k'arar da buhun shinkafa aranar, lemo harda masu siyayya, ashago, siya suka fara Tundaga lokacin komai na mama ya canja, duk abinda take ada, yanxu ukunsa, takeyi, FUTHA wataran ranar daba makaranta, tana zama Lemon dai, ita takeyi saboda ta iya sosai, kullum tafara had'a lemon, saita yiwa Aunty Meemi addu'a, saboda ita ta koyamata komai Haka rayuwa taci gaba, ci gaba, yazowa Mama Anker, saboda yanzu har gida take k'ok'arin siya tabar kasuwa, idan yaso taringa zuwa kasa kayan Yau tana gama komai, haka ta shirya ta tafi makaranta, lokacin suna extra lesson saboda gabatowar qualifying nasu, sai wajan k'arfe 4 ake tashi Lokacin da aka tashi, itada wata k'awarta Khadeeja Taheer, ita tana magana, amma kuma tanada kirki sosai Suna kan hanya, dai dai inda zasu rabu, da khadeeja, zata tsallaka kenan, bata lura da tawowar mota ba, sai jin keeeeeeeeeeeee tayi, duk yanda yaso yakaucemata mai motar Allah bai nufaba, saida motar tayi kanta Keeeeee, saijin k'arar ta Deeja Taheer tayi, tana juyowa sai ganin jini tayi, ga FUTHA yashe a k'asa @ut@r h@jiy@ [11/10, 8:14 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [29/09 8:21 am] @ut@r h@jj@ju✍🏻💅🏻🌹: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussain* *In dedicated to FUTHA Luv* _Page 71-72_ Wata mata nagani ta fito daga cikin motar, da sauri tazo tana tab'a jikin FUTHA, inalillahi " "Yanzu malam idi sai da nace katafi a hankali, amma kaqi, gashi kajamana wahala" Bansan ya zanyi ba, haka dai suka d'auke ta, cikin sauri sai mota Lokacin da Deeja zata tsallako, itama mota ta tawo, shiyasa ta tsaya, kafin ta wuce ita kuma tazo, motar wannan hajiyar taja, sai Asibiti Treatment na gaggawa aka yimata, saboda taji rauni, kuma badan tanacin protein da vitamin ba, da sai ank'aramata jini, saboda tanaci shiyasa ba'a samata Amma dai, ansamata drip, haka Hajiyan ta zauna, wajanta, tunaninta d'aya 'yar waye? tunda ba taga wani sign wanda zai nuna, yarinyar badaga gidan manya ta fito ba Hankalin ta, duk ya tashi, burinta ta farfad'o, taji inane gidansu, dan magareeb takawo kai, kuma duk iyaye nagari, bazaso d'ansu ya kai dare a wajeba, especialy ita da, daga makaranta ta tawo Acan kuma, Deeja bata tsaya ko ina ba, sai runfar Mama Anker, tana zuwa da hakinta, tace Mama FUTHA tayi, hatsari kuma wad'anda suka kad'eta, suntafi da ita Wayyo nashiga uku, abinda take cewa kenan, ya zanyi? wannan yarinya kamar amana take wajena, daga makaranta, ba zama, kai Musa, Isah, kabeeru, saleh kutawo sai nema Haka suka bazama government hsptl amma komai kama da FUTHA babu Hankali ya tashi, FUTHA ta b'ata Acan, bayan k'arewar ruwan da 'yan allurorin da akayi FUTHA, shine yabata damar farkawa, da salati a zuciyarta ta farka, sai ganinta tayi cikin wani d'aki daban, sosai ta watstsake, ta mik'e tafara kallon ko ina, cikin d'akin Turo k'ofar da akayine yasa ta juya, da sauri Hajiyan ta matso kusa da ita, ya jiki tace mata, kai ta kad'a da s'auki, hamdan tace, doctor ne yazo dubatayi yayi yace komai fine, zaku iya tafiya Kafin su fito, daga d'akin, tafara tambayar ta inane gidansu, sosai takemata kwatance da hannu, kenan bebiya ce, wannan kome? tanaji amma bata magana, ikon Allah gata kyakyawa, Amma Allah ya tauyeta tawani part d'in Haka suka tafi, har cikin kasuwa, Mama ansha kuka, idon nan nata yayi ja, kabeeru wanda shi ya kawota shima kuka yake, basu san ina zasu ganta ba, sai ganin tsayuwar mota sukayi kusa da d'akin mama Da saurin su suka tawo, FUTHA ce da bandages a goshinta, da hannunta, taba d'an d'ingisa k'afa Mama ce, ta tawo tace alhamdulillah FUTHA ina kika shiga?, babu inda bamu duba ba, bamu ganki ba, dariya Hajiya tayi, tace a'a da inda baku duba ba, tunda dakunje inda muke zaku ganmu D'akin suka shiga, nan ta bada hak'uri, akan kad'eta da sukayi, sannan tafito da kud'i ten thousand tabayar, tareda maganin ta, sosai sukai godiya sannan ta fito Itafa Hajiya tashiga nazari, da alama matar ta kirki ce, dan babu alamun rashin kamun kai tare dasu Kuma hak'ik'anin gaskiya FUTHA dataji suna fad'a ba yarta bace [29/09 8:38 am] @ut@r h@jj@ju✍🏻💅🏻🌹: To idan hakane, a ina ta sameta?, kuma ya akai suke zaune cikin kasuwa?, dan daga gani yarinyar jinin larabawa ce, ko dai wata qasar Ita kamar gani take tasan fuskar, amma a ina, abinda tun a asibiti takasa tunawa kenan Batada mai bata amsar wannan tambayoyin, haka harsuka k'arasa gida Fadeela tagani, kan kujera budurwar 'yarta, hartayi bacci, sosai tasan tayi missing ganinta, tunda daga, Kaduna ta dawo, shiyasa take cewa Malam Idi yad'an k'ara gudu, akan kada suzo basu sameta ba Tashinta tayi, tace Fadeela tashi, mun dawo, nasan kingaji da jiran mu? Mik'ewa tayi, tace wallahi Mama harnagaji da kiran wayar ki, fatana dai dakika dawo lafiya Amma meyafaru, zama tayi tace kedai bari, garin saurin mu dawo, akan hanya muka bige wata budurwa, amma bataji ciwo sosai ba, munkaita gidan su ma Sosai yabawa fadeela labarin, yanda taga inda suke zaune, hartace wallahi da ace, matar zata bata ita, babu abunda zaisa bazata ru'keta ba, dan yarinyar daga gani, zatayi hankali Amma zansa, asamon labarin ta, dan gaskiya sosai nakejin yarinyar ajikina Haka suka gama, hirar su, kowa yanemi makwanci, dan ko abinci bata tsaya ciba, sallah kawai tayi, suka haye sama ~@ut@r h@jiy@~ [11/10, 8:14 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [29/09 6:29 pm] @ut@r h@jj@ju✍🏻💅🏻🌹: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussain* *In dedicated to FUTHA Luv* _Page 73-74_ Sosai Hajiya Hafsa tafara bincike akan FUTHA, amma a b'oye dan ita gaskiya tana tausayamata ganin a irin gurin da suke kwana Bayan haka, indai ansan cikin garin take, ya kamata afara neman dangin ta, amma zaman cikin kasuwa bai kamaci yarinya kamila irin wannan ba Haka kawai take jin, yarinyar cikin ranta, itama kanta Fadeela labarin FUTHA taji, amma taji ta kwanta mata Shiyasa yau ta dage saitaje cikin kasuwa gurin FUTHA, mama taso hanata, amma ganin yadda ta nace, harda cewa zata gayawa *Yaya Farouq* dariya mama tayi, tace yome *Farouq* zaimun, mutumin dabaya gari, kuma ko yana gari, mutumin daba magana yake ba, ta ina zaki kai k'arata wajan sa? Nidai dan Allah Mama ki barni, haka dai tace taje, amma kada ta dad'e Haka ta shirya, Malam Idi ya kaita, Shopwell tashiga, kayan makeup da undies tasiya mata, sai chocolate Lokacin da sukaje, Mama nakan ciniki, itakuma FUTHA tana ciki, sallama sukayi, Musa ne yace me zaki siya?, babu nazo gurin FUTHA ne, Mama daga can, tace makarantar ku d'aya? A'a ni 'yar matar data kad'eta ne, jikinta nazo dubawa Ohoo, to shiga tana ciki, sosai d'akin gashi k'arami amma yayi kyau, sallama tayi "Wa alaika salam" .mik'ewa zaune tayi, murmushi tayi mata, tayimata alama sannu, duk da bata ganeta ba Zama tayi Fadeela akan kujerar dake d'akin, itadai bata Santa ba, kuma duk zaman datayi da Mama, bata tab'a ganin wani yazo gunta ba Indai ba, mutanen da suke kasuwanci ba, ganin FUTHA na dogon nazari, yasaka Fadeela ta koma inda take, hannunta ta kama Tace, nasan baki ganeni ba, ni 'yar matar data kad'eki ce, labarinki tabani, naji inason kawance dake, kuma na duba jikin ki Ya ya?, ina fatan ban takuramiki ba, kai ya kad'a, kafin me hira suke tayi, duk fa wani abin Fadeela bata ganewa, amma tana k'ok'arin nunawa ta gane Haka suka shantake har la'asar, abinci ta kamata, da lemo, fadeela sai kwano aka bari, ta lamushe komai Waya Ido yamata ta fito, su tafi, kamar kada su rabu, haka ta tafi, lemo roba uku tabata, tunda batada abin bayar wa, idan kud'ine ai daga gani suna dashi Mama ma, sallama tayi mata Zumunci sosai, ya k'ullu tsakanin Fadeela da FUTHA, kusan duk Bayan kwana biyu Fadeela ke zuwa wajan FUTHA, itace dai bata tab'a zuwa ba Labarin yayan ta, kusan kullum dashi ake farawa, custom ne babba, mai aikin tsakani da Allah, yana zaune a Lagos sai bayan sati biyu yake zuwa Yau FUTHA cikin tashin hankali take, saboda Mama garinsu zata koma, dama kud'i taxo nema, kuma tasamu, ba'a garin take ba, tana zaune a Chadi, yak'in da ake agarin shi ya korosu, itada k'annenta, to su sun koma, itace kad'ai a Nigeria🇳🇬, itama jini zata d'aga A b'oye taringa had'a komai, dan kada sugani, sosai take tausayawa FUTHA, saboda tasan idan ta tafi da ita, kamar taqara nisa da ita, da iyayen ta ne Kuma yanzu wazata bawa ita?, hankalinta duk a tashe yake, balantana yanxu da FUTHA tasani, hankalinta yafi tashi Fadeela ce, tazo ganin idon FUTHA tayi, yayi Ja, da'alama kuka tasha, tambayar ta tayi, bata b'oye wa Fadeela komai ba, haka tabata labarin ta, daga lokacin da Kaber ya tsinceta har kawo zamanta a Niger da mutuwar Aunty Meemi, da accident d'in da sukayi (Bazata iya tuna komai, na gidan suba, kota tuna, bazata tantance komai ba) Kuka ta tayata, jin labarin ta, duk da, wani rubuta mata, tayi wani kuma, ishara tayimata da hannu Fadeela ce tace, share hawayenki, dama muna buk'atarki, zaki koma gidan mu, zamu rik'eki da amana, kamar yadda Aunty Meemi ta rik'eki Zaki cigaba da karatun ki, kuma a haka, zamu bada cigiyar danginki Insha Allah zaki kasance abin alfahari wataran, kada kisa damuwa aranki, komai a rubuce yake cikin k'addarar ki, ki godewa Allah, da baki fad'a mugun hannu ba Shekara wajan shida, baka gida, ai abin da ciwo, amma da Allah, kuma baxaki iya tuna komai, ba? Kai ta kad'a, ahaka Fadeela ta tauatae shirya kayanta, hawaye ne yake zuba kawai a idonta Sabo turken wawa, (ko mutuwa ce, sabo akeyiwa kuka, ba itaba), Mama shago shago, take lek'awa sallama, had'a da, Neman yafiya, dan zaman ta awajan shekara 6 kenan, kuma dole akwai wanda zaka b'ata wa, akwai wanda zai b'ata maka Haka aka yafi, juna, tana kuka mutane da yaranta sunayi, haka mota taja sai tasha, inda zatahau motar Lagos, daga nan ta hau ta Chadi, tareda FUTHA dasu kabeeru, Isah, Musa, Bala Fadeela aka tafi rakata Suna tsaye mota taja, wani kuka tasaka, tana tuna abin alkhairin Mama wajan ta, matarda ake fad'in halayenta da masifarta, amma bata tab'a yimata ba Ake fad'ar rowarta, amma ita bataimata ba, komai yimata take, ko yanzu badan tak'i karb'a ba, dubu Ashirin tabata, ganin kamar, [29/09 6:33 pm] @ut@r h@jj@ju✍🏻💅🏻🌹: ranta ya b'aci, yasaka ta d'ebi dubu goma, itama Kabeeru tabawa wanda yakata gurin, batareda kyashi ba, ko bak'in ciki, shima danyaja jari Tunda mama tabar musu, komai na kayan abinci, wani kuma siya sukayi, sosai tayi musu abin arzik'i Haka kowa yajuya, dan shiga mota, wadda suka rako ta tafi, saifatan saduwar alkhairi Daga nan, Fadeela itada driver'n su, basu zarce ko inaba, sai unguwarsu @ut@r h@jiy@ [11/10, 8:18 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [09/10 6:18 am] @ut@r h@jiy@💅🏻✍🏻: *FUTUHATUL KHAIR* *°°°°°°°°°®NWA°°°°°°°°°°°* *©Zainba Y Hussain* *Dedicated to Futha Luv, 'yar mutan Bauchi* *Allah ka d'aukakamu ka kad'aukaka qungiyarmu, kasa mu zama wad'anda za'a amfana da abinda muke rubutawa Ameen, bi jahi habeebe Mohd SAW* *page 75-76* Alu quarters itace unguwar da driver'n da dosa, wayyo dama sokoto da manyan gidan haka, lallai gaba d'aya kaina kwancewa yayi ganin yadda aka keta gidaje, gini a qawace ahaka har muka iso wani katafaran gida, kamar a qasar Kuwait ko Qatar Haka driver yayi hon, da gudu naga wani d'an saurayi yaxo ya bud'e, shi kansa get d'in gidan abin kallone, FUTHA ansaki baki ana kallon gida mai kyau Tunani tafara itama fa, kamar ada can tasan gida mai irin haka, a ina?, takasa tunawa, haka har yaje parking area ya ajiye motar Fadeela ce ta tanjo hannunta, tace welvoe to our resident Futha, ba baki murmushi ta saumata kawai, ahaka suka doshi hanyar main parlour d'in Lokacin da sukaje Mama nakan kujera a zauna remote ne hannunta, tana ganin su ta mik'e oyoyo 'yata sannu, kunsha hanya Kamata tayi, sunkuyar da kai Futha tayi, tsuguwana bakintane yayi motsi alamar gaisheta take, lahiya lou 'yata sannu koh Kusa da ita, ta zauna a k'asa amma, tana d'an wasa da hannunta, Fadeela ce tace, Mama bara muyi wanka, yunwa nakeji wallahi dama banyi break ba na fita, tawo Futha muje Kama hannunta tayi, suka haura sama K'ayataccen d'aki wanda yaji komai middle na yammata bawai na manya ba, na gani, d'akine komai pink kama daga kusan rabin kayan sawarta har furniture da pent na d'akin komai dai sai sanbarka Haka suka Shiga, Fadeela gado ta fad'a tace washa bayana, kinji gajiyar danayi, dariya tai kawai, itama ta gaji,amma bata iya hawa mata gado K'asa ta zauna, ta mik'e k'afa tana d'an matsawa [09/10 8:39 am] @ut@r h@jiy@💅🏻✍🏻: A hankali, ita Fadeela daga kwanciya sai bacci, itama haka, baccin su, suke hankali kwance, especially Futha da aka dad'e ba ayi irinsa ba, ga sanyin AC na bugarta saima qara sakewa datayi take baccin ta Jin shirun yayi yawa, yasaka Mama shigowa dariya tayi, tace kwayi bacci yara, tun safe sai yanxu, kuma a haka bakuci komai ba, idanta yakai kan FUTHA datake yashe kan carpet, sosai yarinyar ta qara birgeta, gata kyakyawa ga gashi kamar India ko larabawa, (a zuciya ta nace ai itace) Tashinta tayi a hankali, ido ta bud'e,murmushi Mama tayi mata, kan gado ta nuna mata, ki koma anan ,zaki gaji, kinji haka ta mik'e ta koma Bacci sukayia, basu suka farkaba sai wajan magareeb, Allah yasa dukkansu suna fashin sallah Ruwa Fadeela ta had'a mata, na wanka sai k'amshi yake, ki tashi kiyi wanka, muci abinci cikina k'ugi yake, bara ni nashiga na Mama Doguwan riga tabata, tace ungo Idan kin fito ki saka, yaya *Farouq* ya siyamun wannan rigar, murmushi tayimata, karb'a tayi ajiye, ta shiga toilet itama Fadeela ta fita A shurye Fadeela tazo ta tarar da Futha a'a a harkin shirya, nima bara kiga in maxa, Mama na jiranmu, itama shiryawa tayi, Humrah ta bata itama tashafa suka sauka downstairs Mama suka tarar kan dining tareda Abban su, gaidashi Fadeela tayi, itama Futha haka, hannu ya kad'a yace lale 'yata sannu koh, kai ta kad'a Abinci ne mai rai da motsi, Tuwan shinkafa da miyar taushe taji manshanu da naman kasuwa manya cikin sa, sai juice na Apple, ganin 'yan gidan kowa nacin nasa, yasaka itama ta zage tana kwasar gara Haka suka ci, suka gama, kuskure bakinsu sukai, aka dawo parlour kallo, suna kallon suna d'an tab'a hira, ahaka har lokaci yayi Mama tayimusu sallama tayi part d'in Abba @ut@r h@jiy@💅🏻👗 [11/10, 8:25 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [23/10 3:47 pm] @ut@r h@jiy@✍🏻💅🏻💦👗: *FUTUHATUL KHAIR* °°°°°° *®NAW*°°°°°° *©Zainab Y Hussein* *_In dedication to FUTHA LUV_* _*~page 77-78~*_ *I'm sorry 4 delay Fans, luv u all* Zaman FUTHA gidan Mama yasa taqara wayewa rayuwanta kuma ta inganta, komai take so ba'ayi mata geji da shi ba Fadeela ma tana iyakar qoqarinta wajan nuna kulawa da FUTHA, Abba kansa ya d'auke ta like Fadeela School kanta sai da aka canja mata, duk da bata Iya maida abu da baki, amma kowa yasan tanada qoqari Bata shigewa qawaye dan tasan ita ba kowa bace, face yarinya mara asali mara gata, mai yawo daga nan qasa zuwa wannan gari Daga hannun wannan sai hannun wanccen Shiyasa ko a gidan, Qur'an kusan shine abokin hiran ta, sai in Fadeela tana nan Yanzu duk wanda yasan FUTHA saiya qara kallon ta, dan taqara wani fari da kyau ga gashinta dayake shan gyara yanzu Hankalinta kwance, duk da ada d'inma hankalinta a kwance yake, amma nan gidan saitaji tafi sakewa ga AC data ke bugunta any time, ga abinci mai hankali Islamiyya agida suke, malami guda aka ka musu itada Fadeela, tunda wanda keyiwa Fadeela yayi tafiya "Mama akullum Idan tana kallon FUTHA, saitaga tana mata kama da wata amma tarasa a ina, shiyasa wani lokacin har pics take d'ebowa ko wai zataga da wadda take mata kama "Idan kaga FUTHA kaga namanta, kamar su d'aya batad'auki komai na Abbanta ba, kamarta da larabawan Libya sak, har tsahon saidai ita NATA farin baikai nasu ba, anan sainace dangin Abbanta tayi Fadeela "Mama ke kwala mata kira," na'am Mamasco, gani nan daga upstairs ta sauko, Mama gani, FUTHA na kamawa gashin ta, kinsan bata iyawa Ok" kuyi sauri mana, kunsan yau Aunty Zainab zatazo kuma gashi kunce dole sai kunje Kano, nibadan kun naceba aida ba kujeba, ga shi Hajiya Zainab tana zataga 'yata Kullum inamata maganar ta, Allah mama Idan bamije yau ba, nasan tafiyan ruwa zata sha Ba komai, kudai fara zuwa Ku amso min alkakin danace Haka akayi suna dawowa daga karb'owa, ko 10 minute basu qara ba driver yajasu sai Kano ta dabo [23/10 4:32 pm] @ut@r h@jiy@✍🏻💅🏻💦👗: Gidan qanwar Mama sukaje, karb'a tayi musu ta arziqi, dan dama ita ta nace suzo, shiyasa suma suka matsa sai sun tawo, next week su FUTHA zasu fara WAEC, shiyasa ko 4 days sukai is ok Sahaf sunan 'yarta, ita qanwar Maman, itama budurwa ce mai hankali, tana buk ma, so tunda suka zo tare ake tafiya school da su, daga nan aje can daga can aje nan Gidajen qawayenta ba'a barshi ba, kullum dai ahanya ake wuni, sun zaga gari sosai Sunje gidajen tarihi na Kano, sunga Dala da Goran Dutse, alal haqiqa garin yamusu dad'i Samari kusan 4 to 5 sai sunyi sallama wajan FUTHA, ita abin dariya yake bata, Idan akace wa ake nema? Wai balarabiyar data zo, to ita Idan ta fita da wani bakin zatayi magana, shiyasa ko taga fita bata yi Suyi, suyi ta fita amma qi take, ita batasan tana zata fara zance ba koda tanada baki, bare babu Haka kowa yake tafiya da sagaggiyar gwiwarsa, Fadeela tayi masifa harta gaji, tace ke Allah yabaki kyau shine kike wulaqanci, ba dad'i amma nasan wataran zaki so wani, shima ya rama Hhhh Sahaf dai dariya take, ganin Fadeela ta d'au zafi, harda dena kula FUTHA Ko gurin kwanciya qasa ta sakko FUTHA tasa pillow da blanket ta kwanta, tare suke da ita a qasa ana kallo, dataga Fadeela bata kulata ba, saitayi tawowar ta, kwalla tafara sharewa tanada kwance Me Fadeela take nufi?, daga bata fita ba zatayi fushi da ita?, ita batasan batason kula kowa ba, saboda rashin dangi, Idan akazo tambaya akace ba'asan danginta ba, ya zatayi daga nan duniya zatasan ko wacece ita Bayan haka, su masu sonta sunada baki, ita bata dashi, ya za'ayi ayi hiran? Kuka tafara tana takura kanta da tuna wani abu ko yaya na rayuwanta, abaya ko ta tuna garin su da sunan Abbanta amma ta kasa bazata Iya ba Sahaf ce tace ke ina FUTHA?, banganta ba, naga da ita ake kallon?, waigawa tayi ita, inata yi to? Fadeela ce tace kyaleta fushi tayi, haka ake mutum yazo gunka amma kaqi ka fita, dan taga tanada kyau ko me? Naga har lecturer naku saida yazo jiya, amma kememe taqi fita, ita ba'akwamaceta ba, sai itace, wallahi bazan kulata ba, Idan yaso ta tafi gida yanzu ma Umma ce tace Fadeela Ba haka ake ba, kuma kedakanki kike cemata haka, idan wani yafada fa, kuma da agabanta kika fad'a bazataji dad'i ba Kya saurari uzurinta, kafin ki yanke hukunci, kuma ke kanki kika kalleta kinsan badaga qaramin gida ta fito ba Kurunga jin uxurin mutum, kafin ku yanke hukunci, yarinya mai hankali da addini, plx Fadeela adena arin haka Kuka naje naga tanayi, kuma yanada nasaba da abinda kikayi mata, narashin kulata da kike Huum, Umma hakane Insha Allah bazan qara ba, bari naje, dayafi kuwa dan bakiyi daidai ba Haurawa sama tayi, qofan abud'e take, shiga tai, ganinta tai takifa kanta a pillow, qarasa wa tai, d'ago kanta tai Akan cinyanta tasaka kan FUTHA, fushi koh FUTHA menamiki kike kuka akan nayi miki magana kibar wulaqanci shine zaki dawo qasa ki kwanta Kai takad'a bahaka ba, huum to yane?, bayani tafara mata akan batason tafita tarasa yazatayi magana, kuma ita suna zuwa wajanta dan basu san ita bata magana ba Bayani tamata, sannan ta ringa bata haquri akan bazata kuma ba Kafin me sai dariya, haka suka kasance har ranar dazasu koma Kuma Ya Farouq shima aranar ko washe gari zai dawo daga Lagos @ut@r h@jiy@✍🏻💅🏻 [11/10, 8:26 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [23/10 7:38 pm] @ut@r h@jiy@✍🏻💅🏻💦👗: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussein* *Dedicated to FUTHA Luv* *page 79-80* Tsit kake jin parlour na gidan. Masu hayaniya basu nan, antafi kasuwa siyayya, anbar Umma ita kad'ai agida FUTHA kinga wani yari wallahi tai kyau, ki d'auka, dariya aka saka saboda yarin wani qatone ga ita kuma batason yari qato Uhum tace Haba hajiya ki d'auka mana zan miki ragi, yana magana yana wani kashe ido Dariya akayi ganin yanda tayi kicin kicin da fuska, jitayi dama tana magana ta zageshi Babba ne amma sai wani kashe ido yake yana matsowa kusa da ita, hannu ta d'aga alamar ya isheta surutun da yake Ganin basu gane ba, fita tai ta tsaya har suka gama suka fito Ko da aka koma gida, labarin aka ringa bayarwa, Umma itama saidata dara tata dariyar Kayansu duk sungama had'a wa, saijiran driver yazo a tafi, Hajiya Zainab taso ta had'u da yarinyar da qawarta kebata labari, Allah baiyi ba, lokacin da taje gidan ta kuma tana libiya, shiyasa basu had'u ba Mama dai tunda Hajya Zainab tazo ta yinarmata taketa kallon ta, takasa sanin ina tasan mai irin fuskanta Haka ta qaraci tunanin ta ta haqura, Hajiya to bakida pic na yarta ki?, lah inada shi bara kigani awaya, hartafara bud'e gallery, akayi mata waya, shiyasa ita bataga pic d'in ba Hajiya Zainab matar abokin Abban su Fadeela ce, lokacin da suka dawo Sokoto da zama suka had'u dashi, abota ta qullu ta tsakani da Allah Matansu ma haka, sosai suke gum inch, su a Sama road suke zaune inda ya tamfatsa gidan sa Shekaransa 3 da tarewa agarin, abokansa suka matsamasa yafito takara, Allah yabashi sa'a alokacin inda ya kasance yacinye kuriar gaba d'aya, akashi 100 yanada 80 A wannan shekara Sokoto tayi sa'ar governor, mai hankali da kirki, ga aiki, ga taimakon talaka Matarsa ma tana taimakonsa da shawara ta gari, shekarar sa 4 yana a matsayin, kafin wani ,zaben yazo Mutane sin so ya qara fitowa amma yaqi, badan komai ba, yanason kasancewa cikin iyalansa amma ba hali, kuma shi baywani son hayaniya sosai, wannan dalilin yasaka shi qin kara fitowa Ayanzu haka shine Senator ne, Abuja yake da ,zama, amma sannu sannu ya dawo sokoto gaba d'aya, kodan garin ya amfana dashi Tunda annunamasa hallaci da qauna a garin, bashida matsala a rayuwa, sai d'aya wadda akullum da ita suke tashi daga shi har matarsa da ita Rashin tilon 'yarsu da sukayi, amma wani ikon Allah saidai suyi tunanin ta, amma ba ikon yiwa wani magana akanta (aikin asirine, wanda baikaryeba) Tanada kirki sosai Hajuga Zainab, qawartace sosai, sunyi wajan 10 years tare, tanada kirki, bata d'aukan kanta wata Yaranta 3 duk maza suna business tare, kaya ake kamu su, kafin yanzu kuma da saidai su bayar ana kaiwa Saudi, senigalies da Atamfa Super da shaddoji a d'inke su ake kai musu Abotarsu sai san barka, kansu a had'e yake kamar ya da qanwa ko wacce tana takatsantsan wajan kiyaye abinda zaika rashin jituwa tsakanin su [23/10 7:50 pm] @ut@r h@jiy@✍🏻💅🏻💦👗: Sahaf bataso zasu tafi su barta ba, tana da biki na qawar tane aminiya miss Hafcy, da babu abinda zaisa bata bisu ba Har da kuka da zasu rabu, ita kanta FUTHA tayi sabo da su, haka motarsu ta d'aga sai birnin shehu A mota tunsuna hira har bacci ya kwasesu, dan akwai tafiya tsakanin Kano da sokoto sosai, shiyasa har sukai baccin su suka tashi ba'azo ba Alhamdulillah sun fita daga gida asa'a sun dawo asa'a, godiya ga wanda yake kare bawansa alokacin da yaso Mama tayi mutuqar murna da dawowar yaranta, bare FUTHA itama tayi missing mama, wanka ko wacce tai akanbaje ana ta bada labarin Kano Mama FUTHA tayi miji, takusa kamiki suruki mai hankali kuwa "Allah sarki 'yata Waye shi a ina suka had'u? Ita FUTHA sakin baki tayi jin zatayi mata qarya ina ta had'u da saurayin, amma bara dai taji wacce qaryan zatayi Mama ai yari da sarqa yake saidawa kinga wani kallo na love daya ke mata, ya mato akanta sosai, saurayi dashi bakinsa Maikyau Dariya ita FUTHA tai jin wannan tsohon akecewa Yaro Ko mama ma dai dariya tai, dataji gaskiyan labarin Huum kinga gobe yayanku zai dawo, saboda haka saiku tanadi mai za'a girka masa Kai Ya Farouq ya kusa, lallai watan fita yawo da cin dad'i, yazo Nan tafara bawa FUTHA labarin yayanta dama dai tasanshi abaki sauran ganin sa @ut@r h@jiy@💅🏻✍🏻 [11/10, 8:26 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [24/10 8:23 am] @ut@r h@jj@ju✍🏻💅🏻💦👗🌹📚: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussein* *Dedicated to Bilkisu(FUTHA Luv)* *page 81-83* Mama ikon Allah flight en qarfe nawa zaibiyo? "Naji dai yace wai sai wajan magbree zai iso gida, amma 4 zai sauka " hum, dama broth haka yake, mu muna d'okin ganinsa shi kuma saiya gama yawansa cikin gari sannan zai dawo gida Ke kuma banda abinki ai ko ya sauka ko da gida yafara zuwa dole dai sai yaje o office nasu na nan, kinga kuwa bagara yagama da su ba? Haka ne to, Allah mam na qagu naga broth 2 month ban ganshi ba Wanccen zuwan da yai duka bana nan, shi kuma nasan murna yake da bana nan Kyaji da shi, ai ya huta kuwa, ba fita kullum muna tare Haka kikace koh?, eh mana Itadai FUTHA murmushi take, komai nasu yana burgeta, yanda suke yin wasa da dariya 4:24pm agogon Niger da 9ja ya buga, adai dai lokacin ne Custom Farouq Yake sakkowa daga airport na sokoto, danzuwa mahaifarsa bayan wata d'aya da sati 2 daya shafe bai ziyarci gida ba " Farouq mutum ne, wanda yasan yakamata yanada hankali, daidai yanada biyayya, rayuwansa simple ce, namiji ne har namiji kyakyawa ne ajin farko, yanada kwarjini da Haiba, da farin jini, ga jajircewa wajan aikin sa, shine assistance chief na Nigerian Customs duka, yana zaune a Lagos inda cibiyarsu take, baya d'aukan hauka ko wargi ga masu hannu da shuni akan kayansu Idan aka kama Baya amsar bravery nd corruption ga kowa, wannan yaqara siyamasa mutunci ya kuma d'auka ka darajar sa Tsayayyene akan aikin sa, rashin aikata mugun hali wa qasar sa itace tasa duk inda yashiga yake da kwarjini Duk wata barazana bata sashi firgita akan abinda yasaka agaba, baya shakka yakama kayan kowaye indai ansami akasin abinda qasa takeson shigowa dashi, Addu'a ta Iyayensa ita take riqe dashi, da tsarin ubangiji amma da tuni saidai wani bashi ba, wannan kyawawan halayyen nasa, sune suka saka yakeda wannan matsayin ayanzu , bawai dan shekaransa yakai ba, abashi ba wannan matsayin ba, a'a ikon Allah da kuma tsayuwa akan gaskiya ruwa da iska Yai fice afad'in 9ja duka, a Lagos yake da zama, amma yana zaga all 36 states d'in, dan ganin yanayin aikin kowa Farouq kenan, d'a tamkar da dubu, iyayensa suna alfahari dashi dama jama'a baki d'aya Qanwarsa guda Fadeela, komai nasa natane, yana sonta matsalanta d'aya tana takuramasa da broth akaini guri kaza, daga andawo taqara cewa nan, sosai yake qaunar ta, wataran suyi fad'a wataran ashirya Iyayensa suna son yai aure, shima haka bawai yaqi bane, amma yammatan ne abin tsoro, suba tangaren bane bare a kwankwasa aga ne tagari, kuma ba kwarya ne suba, yanzu zakaga mace har mace amma halin nata sai a hankali Ansha shine ya warke, ya tab'a yin budurwa Aneesa A Rimi, (Anee), sosai yake sonta itama haka, amma nata Iya bakine, bawai dan Allah take sonsa ba, saidatagama cinye kud'in sa, ya isheta sannan ta fara masa wulaqanci ya sota sosai, bayanda baiyi da ita ba, amma taqi kunsan 'yan katsina da son kud'i Haka yarinyar tamasa, baifi da wata biyu ba, saijin bikinta yai, dama ankusa shine dai tace bara taci kud'insa tayi wasa da hankalin sa Wannan yasa yake tsoran mace, amma duk da haka, baiga wadda tamasa ba, daya fara dating nata *Labari* * * * Saukarsa keda wuya, ya hango driver na gidan su, yana washe baki "Oga barka da zuwa" "Ansha hanya, wallahi kuwa, sannu to Briefcase nasa ya amsa, shi kuma gaisawa ya tsaya gaisawa da mutane wanda yasan su, dama wanda baisani ba, tunda kusan ince 'yan kasuwa sunsan da zaman Farouq Kodan adalcin dayake musu, ga hira dashi da ake gidan TV akan matsalan da ake fama na Brivery and corruption da ake fama Yasan yanzu qananan ma'aikata suna can ana murna, dodo baya nan Ganin zaib'ata lokaci kuma yan son zuwa Office kafin gida, yasa yaiwa kowa sallama ya tafi @ut@r h@jiy@✍🏻💅🏻 [11/10, 8:26 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [24/10 9:30 am] @ut@r h@jj@ju✍🏻💅🏻💦👗🌹📚: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussein* *Dedicated to FUTHA LUV* *Page 84-86* *Gidan Hajiya Zainab* Mami ! Mami na'am yan gidan Mami, ya akayi ake kirana haka Kai wani qayataccen parlour ne nagani yaran sun shiga, kujerune royal na qasar Saudi azagaye aciki, sai labulaye masu kyau, ga manyan prems na gani na fad'a Daga one side Shower ce manya kai komai yayi, gidan senate fa, kuma former governor, abinda yafi haka kaf nagani, part 2 agidan, flowers na gidan Kansu, abin kallone, ga d'awisu da yawa dasu barewa, sunata yawo Gate 3 ne agidan, parlour ba adadi, kowa nasa parlour en yaran daban Mami kinga ya Samad wai dole sai nasaka butter acikin bread en, nikuma kiri kiri zansa, kuma wai sainayi karatu zan farayin break Kai nashiga uku, wai ya kukeso dani, ga Abban kuje wajansa saini, yanzu Ahad yace Halim yad'aukarmasa bike nasa ya fita, kaikuma akan break fast kunzo Mami nayi karatun fa, ba yanda ta iya haka tayi sasanci har kowa ya gane Dariya taji daga bayan ta, uhoo ashe kanjina dasu, wallahi sunfiya rigima daga wannan sai wanccen, kuma kana gani saidai kabarni da rabo To ya zanyi, wallahi Mamin yara nima ina shiga fad'an, guna sukaje, sunfara bayani nace kutafi Mami na qasa Alhaj Abdallah Idan kaganshi daga shi har matarsa bakace sun haifi yara haka ba, kuma bakace sunkai shekarun suba Rigane da skirt na Atamfa exclusive a jikinta, gashin nan an bazashi, ga qunshi maroon a qafanta, abinka da farar mace, komai nata in gentle take Kaikace yarinya yar 25 Idan kaganta, shima haka, yaran su farare tas, su kama sukai da Abban su, fari da gashi na Mamin su Suna a SS 2 ayanzu, yaran ga tarbiyya, saidai fad'a, Dan kullum cikin rabon fad'a take, shiyasa daga anyi hutu ko weekend take turasu gidan Aunty Meenah ko gidan granny Triple ne, shekarun su wajan 13 amma girman jikin da suke dashi kamar na 'yan 17 ko 18 years Abba Ahad ne yake magana Wanda shigowarsa kenan, yes Freind ya kai, dayake haka yake cemusu Abba wai ni intambayeka mana? " inaji, nasan canja machine ne ko system, ko abokin ka kaza bashida wani abu, Ba haka bane To yane? Yauwa Abba ni naji mutane suna fad'in kanada 'ya wai Bilkisu amma ni kaf family indai ba Libya mukaje ba, ban tab'a jin kunyi maganar taba? Kuma naga pics nata da yawa, amma Idan muka tambayi Mami sai kawai muga ta fashe da kuka? Kai Alh Abdallah ta d'aga yace Ahad wallahi ni kaina nakasa tuna komai akan da, nasan dai narasa wani abu mai mahimmanci kuma ko gida naje itama Hajiya zanji tana cewa akwai maganar datake so tayi amma sai taji ta manta kuma takasaiwa kowa magana *(kunsan asirin da akayi, shiga jikin FUTHA yai, kuma an had'a shi da mantau, kowa zaimanta ta, Zainab akayi yafada kan 'yarta, shiyasa tun alokacin ba wanda yaqara maganarat, koda abubuwa sukai normal, shi asirin yana nan)* Sai hawaye shar abin tausayi, ganin haka shima kuka yasa, saida sukai ya ishesu sannan ya miqe Ba tareda yace komai ba 'Yan uwansa ya tara sukai magana, akan Lallai suje wajan Baban abokinsu, malamine babba, ya taimaka da addu'a akan ko menene Allah ya warware, dan saida yawa suna ganin iyayensu cikin damuwa Shawarar tayi, hakan sukai kuwa, driver yakaisu, bayani sukai masa na komai, addu'a itace mafita shima yace, 100k suka ajiye masa akan haka Amma yaqi, yace subari komai ya daidaita Addu'a taci, saidai sadaka da za'a ringa yi Kud'in suka d'iba, Dama ko wanne cikin account nasa ya ciro kud'i, suka had'a 20k dai suka ajiye masa, suka tafi *Farouq* Acan su Fadeela anyi girki, kala kala harda Masar Bauchi, da white rice da stew, sai plantain haka sukayi masa, sai juice da FUTHA ta had'a cucumber juice dana kankana, haka suka shirya table yai kyau Fadeela ce tace wallahi FUTHA kinyi aikin banza broth bayashan juice na had'i, shidai yafison yasha na kwali kona gwangwani, na fad'a miki saida kikayi To ina ruwanki inji Mama, sai kiga yasha, Allah yasa yabaki kunya Haba dai, nasan halin sa, haka sukayi wanka, ita FUTHA abincin taci, ta haye Sama, saboda tanson yin karatu Shikuma saidaya gama abinda ,zaiyi, sannan ya tawo gida @ut@r h@jiy@💅🏻✍🏻 [11/10, 8:26 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [24/10 1:26 pm] @ut@r h@jj@ju✍🏻💅🏻💦👗🌹📚: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussein* *Dedicated to FUTHA LUV* *page 87-90* Unuguwar Alu quarters driver yayo dashi, cikin Wata arniyar motarsa Benz 2016, red colour ce, ga tashin qamshi dayake tashi ciki Ga kakinsa Maikyau daya sha guga kamar sabo, kai kace yanzu ne yasaka kayan baiyi yawo dashi ba Sajensa shine abinda ya qawata masa fuskarsa, system nasa yake dannawa, tana kan cinyansa, ya qame abaya kaikace wani basarake ko wanda muqaminsa yafi haka Sannu a hankali ake tafiya, saboda baison gudu shi arayuwan sa, dats why yake tare da Bakari driver ya iya aikin sa, kuma yasan yanda yake tafi da komai nasa A haka har suka qaraso karafaren gidan su, Horn yai Sani yazo ya bud'e, saida ya Shiga second gate sannan ya murd'a murfin qofar ya fita bayan tsayuwan motan a wajan da aka tanada dan ajiye motoci Laptop nasa da wayar sa yake kwashewa saijin an ruqunqumeshi yai, ko baijuya ba, yasan Fadeela ce Oyoyo broth shine sai yanzu kazo mana, bayan tun 5 yakamata kazo, bayansa ta d'ane tanamasa wannan maganar Fadeela plx ki taimakan ki sauka akaina, wallahi zaki karya ni, narasa matar aure, kinyi qatuwa da yawa Qi tayi, ganin zata gaji dashi yasaka hannunsa d'aya ya juyo da ita, haba sis kinji bayana saikace wanda yad'au Container, waih amma kina aiki, inq zan auri mace mai qiba haka?, ta murqusheni Shidai Bakari dariya yake, yanakuma qara jinjinawa maigidan nasa abisa yanda yake tafi da kowa cikin lumana Broth inamaka oyoyo amma kake mun haka, dankaga ina kewarka, shine zakace wai nayi nauyi, ba ruwana da kai Qoqarin kwace hannunta take amma takasa Hannu yasa ya d'ago fuskanta, yace haba qawalli ta, wasa nake aike bakifi 90 km ba, lalala 90 kace wallahi 60 nake, kaji koh kaqara yankata Dariya yai yace, ni matsa ko uwata bangani ba, ki cika ni da magana, ga shi inajin yunwa To tawo kaci, nasan bacci zakace zakayi, da munje Na.... Bata qarasa ba, yace ba inda zani Dama nasan welcome en da akamun bata Allah bace Wallahi broth ta Allah ce, OK naji muje tiqemun kayana Haka suka jera sai main parlour na gidan Mama fito Broth yazo, naji shi ai, bayan kin tsaremun d'a da surutu Haba mama nid'in, ai yafini surutu, haka ki kace dai Tsugunawa yai, "Mama ina yini munsameku lafiya?, lafiya Lou Umar ya garin ya aikin kuma? Sai alheri Mama, yauwa Allah yaimaka albarka yaqara karemun kai daga sharrin masu sharri " Inye saboda d'ankine kike masa irin wannan addu'a haka, Lallai Ameen to " Abba ne yake wannan magana Gaisar dashi yai, anan suka d'an zauna, daga nan yace Mama lemme go nd take bath, I'm tired sosai wllh Ok, kayi sauri, ga abinci yana jiran ka, tom uwa tagari Wata qofa naga yabi, waje ya b'ullo anan naga yai wani part shima mai kyau, but she plat ne. Key ya cire cikin pocket nasa, anan yafara dubawa haryaga wanda yake nema, sawa yai ya bud'e, wow pink colour shine komai na part d'in, hatta toilet danaga yashiga shima pink ne, Italian bed nasa haka ma Shap shap ya shirya, qananan kaya yasaka, sai turaren passport for love, takalminsa yasaka ya fita A dining ya gansu, shima layi yabi, abincin yamasa sweet sosai yaci ya qoshi Jug yagani akan dining en, yasan ba'a shan lemon had'i agidan shiyasa kawai ya tsiyaya a cup baran daya ganshi fari ne, baki yai dashi direct, instant of yaji ruwa, sai wani irin testing da qamshine ya ziyarci bakin sa, kamar ya tsaya da sha, amma saiya kasa, tas ya shanye yaqara, 2 cup yai yaqara, nunfashi ya sauke wani irin farin ciki yaji, wannan wani irin juice ne mai dad'i, wani jug yaqara dubawa nan ma yaga lemon, baiyi sanya ba yaqara d'aura wa, saida yaji cikinsa na shirin qullewa sannan ya haqura Duk abin nan, Mama na kallon sa, dariya tai tace Fadeela kin kunyata, gashinan mu bamusha ba, ya shanye Me nashanye Mama, juice en nan yanada dad'i, banta6a shan juice mai dad'i haka ba Ya sunansa konakoma can ina siyanshi? Fadeela dariya tafara jin yana magana seriously, Broth had'awa akayi fa, banganeba! Wallahi FUTHA tayi shi, har ina bazaka sha ba, gashi har santi kake Ke bafa wannan jagwalgwalon nake magana ba, wannan da aka zuba cikin jug fah Wallahi yinsa akayi, fad'a masa tai, dariya ce ta kwacemasa Lallai mama kya kallon, indai haka ne kam, to inasonsa Kamar ya tambaya yace wace FUTHA, sharewa yai kawai, tunda baisan taba, kuma bayason tambaya Haka suka ringa hira da gurin aikin sa, har time yai kowa yakama gabansa FUTHA tana sakkowa yana fita, nuni yai ina yake zata gaidashi, ya tafi Fadeela tace, naleqa ai naga kinata karatu, shiyasa bance kizo ba In fad'a miki broth dai yashanye lemon, kuma ya tafi da sauran, aimu bamu shaba, murmushi tai Ahaka suma suka haura d'akin su @ut@r h@jiy@💅🏻✍🏻 [11/10, 8:26 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [30/10 2:28 am] @ut@r h@jiy@💅🏻💁🏻✍🏻💐: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussein* *Dedicated to FUTHA LUV* *Page 91-95* Ko daya shiga d'akin sa brush yai, sannan yasaka boxer da singlet fara qal, system nasa ya janyo yafara bincike akan aikinsa Stool ya janyo wanda ya d'ora mug na lemon Kan kana aciki yana aiki yana sha haka harya gama Baisan ya shanyeba saidaya d'aga mug d'in yaji ba komai, dariya yaiwa kansa Bashi ya tashi ba, sai wajan 1 na dare, bawa idan yagama aikin ba, a'a saidon wayar da Abbansa yasamasa "hello" Abba lafiya da night haka? "Eh naji ajikina bakayi bacci ba, so maza kayi bacci, kada aiki yasaka ka shiga bad conditions, bacci yanada nasa important en So u better get rest plx Omar " Insha Allah Abba yanzu zanyi Yauwa Allah yaimaka albarka Ameen Abba adduar ka garen tanada amfani, a kullum burina naji bakin ka nasamun albarka Allah ya k'ara girma yaja da ran ka Ameen Omar Allah yabaka mace ta gari, yasaka maka da mafificin arziqi mai d'orewa da albarka Ameen Ameen Ameen Abba, ayi bacci lafiya Kit ya katse wayan, yana mai farin ciki Toilet ya shiga, bai jima ba, ya fito sai gado, addu'a yai ya janyo bargo ya kashe light A can Fadeela labarin santin lemon da Ya Farouq yai take bawa FUTHA, dariya tai a hakan dai take tayi magana ta kurame, tace Ya Farouq yanada kirki tunda yasha abin da nai Huum harkin bashi lambar yabo, wallahi ba wani kirki gareshi ba da yawa ba Kai ta kad'a kawai, a haka sukayi baccin su mai cike da farin ciki Safiya nayi kafin Fadeela ta tashi hartayi wanka, ta taimaka wa Iya Ladi da aikin gida, kafin 7:30 tayi driver ya jata sai IMAN INTERNATIONAL SCHOOL inda nan aka maidata bayan dawowar ta gidan Yanzu exam ba kama hannun Yaro ita take sun gama WAEC sauran NECO, lesson suke shiyasa taje 10:00 kowa ya fito cikin shirin sa, danyin break fast, Yam balls ne sai tea mai kayan qamshi da na'ana ga qamshin lemon grass dayake tashi, plantain a soye itama Kowa zama yai, gaishe da Iyayen sukai, bayan nan Fadeela tayi saving nasu cikin plates Madara ta d'akko da Milo ta ajiye kowa ya zuba dai dai shi Harya janyo madara sai yaji bara dai yasha a haka, wow so sweet whts kind of tea na Mama do 4 us Ba magana haka kowa ya sha batare da madara ba, a tare suka dire cup alhamdulillah wannan tea haka? Nima abinda zance kenan, wallahi nidai ban tab'a shan shayi mai dad'i haka ba, Mama kina mana shi plx To ba Mama tayi ba, FUTHA ce, dan ita ta Iya komai, kaci yam balls en nan kaji? D'aya ya d'auka bakinsa yai, lumus aifa saida Abba ya riqe hannun sa yace kabarshi haka, bazakayimana irinta jiya ba, ka shanye duka lemon, yanzu ma Ka cinye yam balls d'in nan ba Inasonsa FUTHA ta iya girki, tsayawa yai yace Abba wace FUTHA? new house gal ce ko kuwa Amma koma mene ta iya girki, ace ina gaidata Yana gama fada ya miqe bai saurari jin wace FUTHA ba Kwanan sa goma agarin yanxu ma yana shirin tafiya wajan aiki, bai tab'a had'uwa da FUTHA ba, itama haka Duk lokacin da zasu had'u sai wani sab'ani ya gifta, gashi girkin ta ya namasa dad'i, ya lura ta iya girki Baitab'a neman taba, saboda a tunanin sa house gal, ce amma wataran Ji yake kamar yace a kirata yai mata kyauta Amma baiyi hakan ba, Fadeela bata tab'a lura cewa basu had'u ba 4:00pm dai dai lokacin ne driver'n Farouq ne ke driving dan kaishi airport zai koma aiki ta Titin BYPASS suka biyo anan IMAN take school d'in su FUTHA FUTUHATUL KHAIR ita alokacin suka fito tareda qawayenta STYLICH da PHARTY BB, tafita take tanata dariya saboda wata magana da sukai akan qawarsu NAFEE ANKER Fuskanta smooth tana kyalli take washe baki ga school uniform d'in ya karb'eta Shikuma daidai lokacin yasha kwana da fuskanta yafara arba Hasbunallahu wa ni'imar wakeel, Allah yayi hallita Jiyai jikinsa ya tsaya cak, kafin ya farga ya nemeta ya rasa, ihu yasaka plx driver back back Kayi sauri kada ta ba'ace haka yai gudu, yammatan yagani amma kamar ba ita?, hakan ce ta kasance dan babu ita Zagaye wajan sukai amma ba ita Haka ya qaraci duba dubensa ya ce a tafi fuskansa cikin yanayi na rashin dad'i @ut@r h@jiy@👱🏻‍♀ [11/10, 8:26 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [30/10 8:42 am] @ut@r h@jiy@💅🏻💁🏻✍🏻💐: *FUTUHATUL KHAIR* ______*®NWA*_______ *©Zainab Y Hussein* *Dedicated to FUTHA LUV &Anee Maman Ayman Aseef habeebaty ana bihibak bikil Hayatee* *Page 96-100* Shi kansa driver'n ya lura oga kamar yana d'an neman wani abu, gashi basu ganshi ba Haka har suka isa airport ya direshi ya juya shi kuma ba wani jimawa jirgi yazo aka fara Shiga FUTHA lokacin da suke hira adaidai nan driver ya qaraso d'aukanta shiga tai yai gaba, shine dalilin da yasaka baiganta kusa ba Ko cikin jirgi dariyar ta yake hanga da siririyar wushiryarta mai ban sha'awa Bayan kwana 2, yau gidan Aunty Zainab zasuje shiyasa ko Malam na islamiyya suka masa waya kada yazo, FUTHA ita tunda aka ambaci za'a gidan hankalinta ya tashi tarasa sukuni addu'a take yi azuciyarta kawai tasan duk tsanani itace maganin komai Su Ahad da Waheed haka suka kasance suna zuwa wajan Malam addu'a kullum da saukar Al Qur'an ita ake, sai rubutu da ake yayyafawa cikin gidan Alhamdulillah sunga sauyi dan sau dayawa damuwar da suke gani afuskan iyayen yanzu babu ita sosai Kuma dukka pics na FUTHA da aka cire tun kafin Haihuwar su, sun d'akko sun goge sun maidasu kusa dana iyayen Hajiyansa kanta yau sai gashi Allah yabata ikon cewa Bilkisu ta b'ace kenan babu maganar ta? A daidai lokacin ne kuma, acan katsina gidan su na farko ana gyara Gidan aka tone wani qulli kamar bazasu bud'e ba masu aikin sai kawai sukai shahada, Innalillah wata laya qatuwa sai gashin akuya baqa kuma ga hayaqi daya fito addu'a suka fara anan wani yai shahada yasaka ashana ya k'one kayan Sallah FUTHA keyi, bayan ta fito daga wanka ayi shirin tafiya gidan Aunte ZAINAB, fit taji ajikinta kamar fitar allura cikin tsoka taji zafi Sai kanta daya juya, ahaka ta sulale ta fad'i awajan ba tareda sanin kowa na gidan ba Fadeela akai sa'a ta shigo saiganin mace tayi yashe a k'asa ba alamar numfashi, kuka tasaka Mama kizo kiga FUTHA ta mutu wayyo Allah Da gudu itada Abba suka haura upstairs girgizata sukai shiru, haka ya d'auketa sai Asibiti dan jin ko menene Abdul Abdul BILKISU 'yata ina kaganta wayyo Baby were ar u?, kizo ga Mama Nan da nan aka taru kowa kuma saiya fara tuna FUTHA, tana ina? basu sani ba shekara wajan 13 innalillah a ina zasu nemeta? Me yasaka suka manta da sanyin Idaniyr su?, nan fa kowa yashiga tashin hankali baran pics nata da suka gani a parlour ma'aikatan gidan wajan Su 12 kowa jimami yafara Ana maganar ne Hajiya da Aunty Meenah suka shigo suma ina FUTHA?, kururuwa aka fara ina zasu tarki nemanta?, kuma gurin wa? Parlour suke tafiya saijin hayaniya sukai, ana dubawa CHUCHU ce ta shigo a hargitse, tana shikenan Bilkisu kin cuceni kin kassaramun rayuwa, wayace a tone wajan, boka yace bazata dawo ba, ta tafi kenan Kutmar yau zanga shegen daya tone layar danasaka ita kuma tayi addu'a asirin jikinta ya karye Zainab kin zama muguwa duk abinda nake saida kika tona, kai Mama kin cuceni, sumbatu kala kala Kowa kuma ya fuskanci itace Ummul aba'isin saka FUTHA cikin bala'i tayi sanadiyyar rabata da mahaifar ta Abdul ne kuka ya kwacemasa yace CHUCHU kin cuceni Allah ya isa tsakanina da ke, burinki ya cika ada, amma ko adan baiyi tasiri yanda kike so ba Mari yafara bata yace ina takaimasa 'ya maqurar dataji yasa tace kayi haquri nayi dana sani, tana Niger nan nasaka aka kaita Numeiy aka ajiye ta, aaaaà tana qoqarin magana amma takasa Asirin ya koma kanta, tazama kurma sai kuka take dama ta yamushe tazama wata tsohuwa Abba kuka Zainab dasu Hajiya kuka ina zasu fara nema?, Abban FUTHA shine yace ba jira aka hanya atafi Niger Basuyi gaddama ba, Motoci aka d'iba aka tafi Likitoci ne kan FUTHA suna qoqarin daidaita numfashinta wanda ya d'auke Idan kuma ya dawo saiyafara sama hakan yasaka su b'ata lokaci akan ta Fadeela ita hawaye takeyi, tace Mama lafiya nabarta tana Sallah to mene ya sameta? ba amsa Alhamdulillah FUTHA ta farka da salati a bakinta, kama bakinta tai magana tafara a hankali nan taga maganar na fita, kabbara tai da qarfin gaske Lallai dama tanada rabon qara magana Allah Hakeem Mama ce tashigo, FUTHA kin tashi sannu, Yauwa Mama Eye! FUTHA kekikayi magana!, nice Mama kabbara tafara da godiya ga Allah mai iyawa, ahaka Fadeela tazo ta same su Tashi FUTHA tai ta rungume Fadeela tace Fadeela dama zan k'ara magana Fadeela ikon Allah ya sauka a kaina ina sallah najini wani iri kafin na farga Jikina yai weak bansan komai ba, sai yanzu dana ganni maybe nafad'i ne Rungume juna sukai tanaimata murna, baki rahma ne, jin muryanta siririya mai dad'i saikace ana busa sarewa Amma daga ji FUTHA ba real Hausa bace dan muryanta hausan bata fita sosai, koba komai jikin ta ya nuna itad'in wani yare ce Allah cikin Ikonsa ya kaisu Niger lafiya, da pics nata suka fara bawa mutane ko sunsan wannan yarinyar tana qarama 13 years ago, babu wanda ya gane ta ko ya santa, harsun juya sai su kaga wani, nuna masa sukai Yana gani yace kai ai yarinyar data cinyemun abinci ne a wannan garin Nan yabasu labari, murna suka fara jin cewa yasan gidan mutumin daya d'auke ta dan shekara 4 ma sun had'u Haka suka tafi garin Abalak, gidan yana nan, sai canje canje da aka samu Tambaya sukai wani yace baisan taba, amma ga Gidan Alhaji Raheem suje Sallama akayi dashi, baijima ba ya fito, gaisawa sukai sannan suka fara fadamasa abinda ke tafe da su Allahu Akhbar Ikon Allah Allah mai axirtawa ashe yarinyar nan yar babban gida ce, har sun fara murna sai gani sukai yafara share hawaye Nan ya zayyanemusu zaman datayi, kama daga zuwanta har ranar da suka tafi Hajiya ce tace kenan sun tashi daga nan, Sokoto suka tafi, muma daga can muke Ayya ai aranar 16-7-2013 sukabar garin nan aranar kuma Allah yai ikon sa akan hanyarsu mota tayi accident babu wanda ya shura acikin su Gara kabeer an ganshi, ita gaba d'aya FUTHA qonewa tai ko gawarta ba'a samu ba Tokarta da babban d'anyatsanta sune aka gani, akayiwa sallah aka bine Mekkkkkk......kafin kace me ta tafi luuuuuuu mamanta ta fad'i @ut@r h@jiy@👱🏻‍♀💅🏻 [11/10, 8:26 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [31/10 3:48 pm] @ut@r h@jiy@💅🏻💁🏻✍🏻💐: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussein* *Dedicated to FUTHA LUV* ~*page 101-105*~ Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, wannan wace irin rayuwa ce? Daga wannan sai wannan, ruwa aka d'ebo aka zuba mata ajiyar zuciya ta sauke hawaye mai zafi shiya ciga ba da zuba a idaniyar ta Yanzu kenan sunga samu sunga tashi, yarinyar ta ta mutu, batada rabon ganin ta Kuka itama kanta Hajiya tayi, saboda ayanzu taji tana qara qaunar jikar ta Basu zauna ba haka suka kamo hanya zuwa sokoto tunda basu samu abinda suka zo nema ba A motor sai rarrashinta suke akan ta d'auki qaddara, Hajiya wallahi inaji ajikina BILKISU tana da rai, amma nabarwa Allah komai shi yafi ni sanin abinda ya b'oye akan ta Yauwa haka suke tafiya ransu ba dad'i, Abba kansa daure wa yake, dan shi yafi qaunar Bilkisu akan sauran yaransa tun kafin ma samu yaran A can murna dai FUTHA baki ya bud'e, takasa sarrafa murnarta sai dariya take, a haka suka tarkata sai gida Hajiya Zainab taji d'aci da ciwo na mutuwar 'yar ta, haka ta kasance sukuku har bayan komawar su gida A gidan Mama sunkasa zama daga suyi ta mata magana dan suji muryanta saisiyita waqoqi, Fadeela ita ganin abin take kamar cikin mafarki Mama da kanta tarunga bugawa 'yan uwanta waya suna tayata murna, Sahaf itama saiga wayarta sun jima suna magana Waya Fadeela ta d'auka tace Broth FUTHA bakin ta ya bud'e tana magana I'm really happy Huum sisto wace FUTHA kindameni da ita?, komai na abinci ace itane tayi wace ita? Yaya tsintar ta akayi fa, kuma tanada kirki gata kyakyawa kamar Balarabiya , maganarta kamar sarewa dan dad'i Anya kuwa duk kyanta Bata kai 'yar makaranta ba, komai ita ta had'a, duk da kallo d'aya namata Nan yabata labarin yarinyar, ayya broth zaka ganta insha Allah, ashe broth he fll n lv, lallai to Allah yasa aganta ko mayi biki agidan mu Haka suka fara hira, ya manta yace abashi FUTHA su gaisa, duk da baisan taba Tafiya dai tasha ruwa dan sun manta da wata Hajiya Zainab da gidanta da zasu, sai wajan 8 sannan FUTHA tace Mama anmanta da gidan qawarki Wallahi kuwa aje wataran, Yau ai ranace mai tarihi da farin ciki a wajan mu Amma FUTHA zaki Iya sanin sunan garinku da Abban ki? Kai ta d'aga (kunsan dama harda mantau aka saka mata)(amma koda babu Mantau a shekarunta bazata iya fadar wani information Maikyau ba) Mama nasan dai Baby Maman mu ke cewa, then a Katsina muke amma daga nan bansan komai akai ba Mama na a Libiya take, muna zuwa, da Abuja wajan Aunty na Yauwa to a katsina wacce unguwa Abban ki kuma ya sunan sa?Mama ke tambayar ta Abba kawai ake cewa, haka dai sukaita tambayar ta ita kanta taso ta tuno wani abu amma ta kasa Haka zamanta yaci gaba, HAJIYA Zainab taiwa Mama waya akan batada lafiya sun tafi garin su Sosai ta jimantamata akan Allah yabata lafiya, bata fad'a mata cewar ga abinda yasameta ba Saboda batason tunowa, yawan maganar shine yasamata ciwo, gashi jininta har yakai 200 abinda ba'aso kuma Ya Farouq acan bashida tunani saina 'yar makaranta, har ya dawo yana tuna ta, wajan kwana 2 yana zuwa qofan school en amma Allah baisa ya ganta ba Yau yana CBN qrts gidan su Leemcy wanta abokin sane, kamar ance d'aga kanka itace cikin motor suda Fadeela, motar bata Gidan su bace, ita yagani kad'ai ba Fadeela da gudu ya tashi,amma ina kan yaje sun qule Abin tausayi ayanzu duk wanda yasanshi yasan yanada damuwa ko Mama tayi tambayar shiru Yau wajan shopping yaje itama haka, lokacin ita tare suke da class mate nata, tunda sauran kwana 2 candy nasu shine aka zo siyayyan gift wanda zasu bawa teachers nasu A wajan cashier suka had'u, matsawa yai kusa da ita, jikinsa har rawa yake ganinta da wata baqar abaya anyi rolling ga kanta yai tum, ga giranta baqa data qawatamata fuska Yana qarasa wa har yace yammata........ sai qirr yaji Waya, kamar bazai d'aga ba, saboda yaga har anfara musu lissafi suna biyan bills OMG ogansaneke kira da sauri ya d'aga dan yayi yayi yagama wayan ya juya Saidaya qare sannan ya juya wayam, innalillah, dubawa yafara harda fita waje amma shiru ba ita ba labarinta Hankalinsa ya tashi, sosai yafara tunanin kodai aljana take masa haka?, bashida answer Mama ce Yau dai tasha alwashin lallai sai anje gidan Hajiya Zainab suyimata sannu da kuma gaisuwa had'e da jaje, Maigidan ta yagayamata komai Haka kuwa duk suka shirya @ut@r h@jiy@👱🏻‍♀💅🏻 [11/10, 8:26 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [01/11 6:09 am] @ut@r h@jiy@💅🏻💁🏻✍🏻💐: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussein* *Dedicated to FUTHA LUV* *page 106-110* Fadeela ta riga FUTHA shiryawa, tana tsaye dai tana kallon ta, ganin madarar kyau da Allah yabawa FUTHA, akan stool take amma sai gani nayi ta miqe da sauri D'akin Mama tai, Mama!Mama! na tuno wallahi natuno Me kika tuno Fadeela?, mama wallahi FUTHA 'yar gidan uncle Abdallah ce, Mamanta Hajiya Zainab, kuma kinji tace a katsina suke, before suma a katsina suke, kuma ina yayar sa Aunty Meenah a Abuja take, Libiya garin su Hajiya Zainab itace ga kamarta da ita kamr antsaga kara Ajiyar zuciya Mama ta sauke, tace Ikon Allah, wato Allah Idan yaso ya jarrabeka abu yana kusa da kai saiya hanaka ganin sa, wallahi tunani na a kullum nasan fuskar FUTHA amma a ina?, shine abinda nake kasa tuno wa Allahu Akhbar Allah mai girma buwayi gagara misali, mai hikimane shi cikin Hikima Allah Hakeem, wato itace Bilkisu wadda nakejin labarin ta b'ata, bana ita tagayan ba A family nata na Libiya da sukazo ake maida zance Wallahi itace ga kama nan, Mama ina zaune kawai na kalleta saina hangi Fuskan Aunty Zainab, aisai muyi sauri mu tashi Allah yasa abinda muke zargi dai dai ne Ameen Fadeela tace, bakinta yakasa rufuwa FUTHA zataga iyayen ta, kai babu abin godiya bayan Azzawa jallah Ke Fadeela ki rufe bakin sai dariya d murna kike, Hala Abdulaziz yace yana so, hhhh bansani ba inadai farin ciki ne Huum ni kuma kinga jikina some how nake jin sa, kamar wani abu zai faru amma na murna banjin baqin ciki ne, tun kwanaki sainayita mafarkin wata mata da yara 3 amma bayansu ajuye sunata laluba ciyayi Idan naje sai naga sunmun nisa Jiya kuma har wajan su na qarasa na zauna kafin muyi magana akayi kiran Sallah, shine jiki na duk ya mutu Kafad'arta ta dafa tace komai yazo qarshe insha Allah, wannan matar ba kowa bace illa mahai....... Fadeela ku fito inajiran ku, maganar dabata qarasa ba kenan suka fito A'a yammatan Mama haka kukayi kyau, lallai munkusa shan biki, dariya sukai amma ba wadda tai magana Da adda'u suka shiga motor, baran FUTHA da qirjinta sai fat fat fat yake mata, dannewa take kawai Hanyar Sama road suka nufa gidan Alhaji Abdallah Mai Nasara, babu wanda yai magana cikin su, ita mama addau take Allah yasa haka ne, itama tasamu real parents Itama kanta Hajiya Zainab tana zaune akan carpet kallo suke amma ita idontane akai hankalin ta baya wajan, Ahad ne ya tab'ota yace Mama lafiya? naga tun d'azu kamar ba kallon kike ba.Ahad wani iri jiki na yake, kamar zanga wani abu, ko kuma zan rasa Insha Allah alkhairi ne, kidena saka damuwa Allah zai bayyana Aunty indai har tana raye, kiyawaita addu'a kuka qin cin abinci, tunani duk bashi zaisaka Allah yaka mafita ba, addu'a itace babbar mafita Hakane Ahad Allah ya rayamun ku, Ameen uwa ta gari haka suka ringa keta gidaje masu kyau har Allah ya kasu qofan dazata sadaka da gidan Horn sukai akazo aka bud'e Already dama ansan su, ba maganar bincike ko wajan wa aka zo Da qarfin gaske daga Maman FUTHA har ita sukaji bugun zuciya, kamar ta juya FUTHA amma ba hali, haka suka jera kowa da abinda yake saqawa har suka isa parlour d'in [01/11 6:20 am] @ut@r h@jiy@💅🏻💁🏻✍🏻💐: Assalamu alaikum, ga baqi ba notice Haba dai wani notice jiya nake cewa yau zanzo fa, saina tashi jikina a mace Marab....... d'agakan da tayi shine ya hanata qarasa fad'an abinda ta ke so HAJIYA menake gani a bayan ki, BILKISU ce wallahi 'yata ce aka ce ta mutu ga kama nan sai kuka Itama lokacin da tayi arba da Mama jitayi a duniya ba abunda take so sama da ita. taga ne Maman ta, ga kama ma nan, da gudu ta qarasa tace Mama ! mama ! Nice Baby Mama kina raye baki je kin duba niba, ina Abba yake Mama nagane ki kece Mama na, Mama ina Abba meyasa baku qwaceni wajan Aunty Chuchu da zata tafi dani ba? Fadeela mama na kenan, wallahi itace ina mafarkn ta fuskan Mama bai b'acemun Mama ina Babyn mu ko baki haifa ba? Gaba d'ayan su jikinsu rawa yake, kowa kuka yake ita FUTHA takasa sakin Maman ta, sai wani qara riqunqumeta take yi Wata irin soyayya da qauna ta d'a da uwa itace take sauka a jiki da zuciya na wad'an nan bayin Allah Sosai suka ringa koke koke na murna, Mama ce ta tab'a bakin ta tace Baby yana ga kina magana? Mama ban jima da farawa ba, Ina garanny Mama? Bata rufe baki ba, tajiyo hayaniya sune Waheed ne ya musu waya akan suzo anga Aunty @ut@r H@jiy@👱🏻‍♀💅🏻 [11/10, 8:26 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [01/11 8:44 pm] @ut@r h@jj@ju👱🏻‍♀✍🏻💅🏻📚📝: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussein* *In dedication to My Friend Sadiya Abdallah Shehu(STYLICH BICH), Wllh I dn no ur love to me is highest, u care about me nd ma love once, may almighty Allah protect, assist u n guide u among ur evil, u r indeed d greatest Stylich u support me aloot, love does nt care abt money or beauty, our love is generally 4rom Rabbis samawati I'm out of word Stylich, may Allah SWT bless u wth great personality husband, nd bless u too wth good Children, I love u, I love really appreciate wth ur good prayer to me, Ma STYLICH nd Ur Blood sister Ya Hajja. Ya Allah bless STYLICH wth powerful health Ameen* *page 111-115* Hajiya da gudu ta shigo, tana cewa Allah Hakeem da gaske anga Bilkisu?, tana shigowa da ita tafara cin karo Habawa da gudu taje ta rungume ta, tana kuka BILKISU ki yafeni wallahi bada sanina nayi miki abinda nai miki ba Bilkisu kina raye, akace kin mutu, munje Har NIGER gidan Alhaji Raheem yace kunyi accident, Baby kece tana magana tana shafa fuskan ta Gaba d'aya jitayi ko yau Allah ya d'auki ranta tacika burin ta taga iyayen ta, cikin aminci, lallai Allah shi keda IKO Abbanta ma sai gashi shida Abban su Fadeela, waya akayimusu, ahaf wani sabon kuka da murna su suka qara samun waje acikin gidan Abban su Fadeela yace Allah qadiran wa maridan wa hayyan rayayyen sarki, wato 'yarka tana gida na amma Allah baibamu ikon gane taba Nan fa hira ta sarqe FUTHA tana kusa da Abban ta (Dama yana qaunar FUTHA sosai) Qannen ta dukkansu haka suka ringa zuwa suna mata murna, kafin me saiga 'yan uwa da abokan arziqi, sun cika gida Mutane basu ragu ba, sai da akayi sallah ta Magreeb, abokan Abban ta nan ma kowa yazo yayimasa murna Aunty Meenah itama Sai gata, anmata waya flight ta biyo, kai Iyaye rahma FUTHA jitayi kamar da can wani Abu baitab'a faruwa ba Basu sami damar magana da Mama ba dole sai da safe tace zata zo, Fadeela fuska tai tace itada qafarta qafar FUTHA bazasu rabu ba Haka Mama ta tafi ita d'aya, tana mai farin ciki da murna Kwana tayi da Iyayenta anamata sannu, ana bata labarin abubuwa 'Yan uwan Maman ta suma ayanzu haka suna cikin jirgi dan zuwa ganin jikar su, da 'yar su Haka akayi washe gari da wuri Mama tazo, anan ma tayi breakfast ita da su Nan Maman FUTHA tace Hajya banda bakin godiya duk abinda zance ban biyaki da shi ba, Illa iyaka nace Allah ya qara had'e kan mu Ameen tace, Huum nifa bansan da gaske cewa 'yarki bace, ashe haka ne, amma ya akayi bakwa maganarta sannan ta b'ata baku nemeta ba, sai yanzu? Kuka Maman FUTHA tasaka tace Allah ya isa tsakanina da Chuchu ta cuceni ko da yake kanta tayi wa, dan gashi ni yanzu sai dai labari abinda tayi ya jute mata itada uwar ta da uban ta Huum, to ai Hajya ya akayi, yarinyar Ku tab'ata kuma kuka mance da ita? [01/11 9:11 pm] @ut@r h@jj@ju👱🏻‍♀✍🏻💅🏻📚📝: Kuka Hajiya Zainab tasaka tace *TUNA BAYA* Lokacin da FUTHA ta fita bansani ba, nayi zaton tana garden ko study room, har dare ban ganta ba, ganin lokaci ya ja, gashi Abban ta ya koma gidan jiya ba halin magana, saina yi zaton ko tana gidan Hajiya Haka dai har dare, muna abu d'aya nida 'yar kina, ganin shirin yai yawa yasaka naja motor sai gidan Hajiya, hankalina atashe na shiga, mugun ji wai bata nan, kuka nasaka Kafin Safiya naci kuka na qoshi haka na tashi nayita sallah da addu'a akan Allah ya bayyanamun 'ya Safiya nayi, nafita ba inda banjeba inda nasani banganta ba Abban ta kuma waya ban izini bare naganshi har na fad'a masa, haka har wajan one week ba labari gidan Hajiya ko naje sai daitace Allah ya bayyana amma ba wani duba ko magana mai dad'i, ko ta nuna damuwar ta Gidansu Chuchu naje nan ma ba fuska, Illa dariya da shewa da aka mun, gashi lokacin cikina ya girma, ban Iya komai ga cuta ta ciki ga damuwa ta rashin 'ya Chuchu Murna take, harwani sabon wulaqanci ta qaro, banda halin ganin miji gashi a Asibiti ana son ganin sa, saboda since CS za'a mun Gashi shiru, nakasa fad'awa gida, 'yan wajan aiki na, sunmun kara dan har garuruwa suke tafiya da pics nata Amma shiru ba labari, Allah maji roqon bawansa nakama naquda bata nan lokacin, komae ya shigo dashi d'akina oho, haka ya shigo ya ganni a haka Asibiti muka nifa, Na wahala na galab'aita dole akace yasaka hannu CS za'a mun Kud'in yatafi d'aukowa dama ya shiga dashi gida jiya, nan ya duba baigani ba haka yasa ya d'aga gadon ta Waih addu'a ita tazo bakin sa, abinda yagani ya d'aga masa hankali, d'aukowa yai ya qone, itama acan house gal na Chuchu ta d'akko wannan leda ta yar ta yimata filla filla Shidai yana tsaye sai masu gadi ne suka ga ya fad'i, daidai lokacin Hajya tazo Asibiti akayi dashi, nan fa akayimasa agajin gaggawa, wata nurse ce tafito take tambayar ina wanda yaka wata mata, Allah Raheem maganara kamar a kunnansa haka ya miqe Hajya na bin bayansa Yara uku ta Haifa batare da anyi mata komai ba, murna nan Hajiya tafara kuka tana neman gafara ta Banja da nisa ba, tunda nasan aikin sihiri ne, yafemata nayi daga ita har d'anta @ut@r h@jiy@💅🏻👸🏻💁🏻 [11/10, 8:26 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [02/11 8:45 am] @ut@r h@jj@ju👱🏻‍♀✍🏻💅🏻📚📝: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussein* *Dedicated to FUTHA LUV* *Adda Bena Yau ban hawa online, bare nagamu da ke, Jabo ta zugaki nasan balinta, ina off yau hhh* *page 116-120* Sosai Abdul yai murna da yaran, haka muka tarkato sai gida, Kowa yana murna amma ni zuciyata a cunkushe take saboda b'atan 'yata Hajiya da kanta tamun wanka ta gyara yaran, tayimun Tuwo da Miya sai kunun kanwa, ko data kamun ban iya sawa abakina ba inacan tunanin Baby Kafad'anta Abdul ya tab'a yace Maman Baby kici abinci mana then saikiyi tunanin nasan bana komai bane saina abinda nayi miki nasan badan haqurin ki ba, wallahi bazaki yafeni ba Nazamto macuci a gareki na danne miki hakk'in ki na yasar da 'yata na cuceta dan Allah kuyi hak'uri Ku gafarcen ba yin kaina bane plx Matar arzik'i? Kuka na fashe da shi nace na yafemaka duniya da lahira, Amma Baby ta b'ata wajan 6 days kenan ba'a ganta ba What! kina hauka innalillah wannan wacce irin masifa ce, bashiri ya bazama Sai nema Danginta suma sunzo da su aka ringa nema amma har tsawan sati biyu ba labari, haka na ta rame na d'ashe bancin abincin kirki addu'a itace abar yina ko wani lokaci Abban ki saiya zamo nafishi dauriya kullum cikin tashin hankali yake baya Iya cin komi Rarrashi shine nawa, da ban baki duk da nima ina buqatar mai kwantarmun da hankaki Chuchu koda tazo gida dayake bata nan, hankalin tashe dataga kowa a dangi ya koma yanda yake mun, gashi Abdul ko sauraronta baiyi ba A ranar dataje d'akin sa duka ya mata, shi baisan wacce k'addara ce tasaka shi auren Chuchu ba, da da hali daya tsigeta a rayuwan sa Lokacin da masu gadin gidan suka rink'a bashi labarin abinda yayiwa Zainab kuka ya k'ara saki, lallai Zainab mace ce ta arzik'i Maman Chuchu dai komai yafara lalacewa dan Abban nasu yafaramata wulaqanci, kafin wani lokaci asirin jikin sa ya karye, nan itama yacimata mutunci yai kuka akan rabashi da tayi da wansa da family nasa Gashi ta b'ata masa yara, babu na zab'e cikin su, ita ma Chuchu miji babu shi yamanta da ita Munyi nema munyi nema har ba adadi, Abban Chuchu shine yaji lokacin da suke magana akan itace tasaka aka b'atar da BILKISU Nan fa yazo yagayamana aranar Chuchu tasha duka koni danakeda d'anyen jego sai dana daketa, kuma yace ta fitomasa da 'ya Hajiyansa kaf sukace court itace zata rabasu da ita Dukan da taci shine yasaka taimaza taiwa wanda tabawa Bilkisu ya yar akan yaje yazo mata da ita Tsit ba labari, gashi lokaci yana qurewa, ganin bazatayi nasara ba yasata Shiga malamai akan tanaso ayimata d'aurin baki adena maganar FUTUHA Allahu Akhbar wallahi tundaga ranar ban qara magana ba, Har dangin Abban ta gara dangina suna magana Tsafi gaskiyar maishi dan haka tayi mana, amma wani ikon Allah daga ranar bata k'ara samun dama kan kowa ba Tayi zaman shekara biyu lokacin yarana sunyi kwari, Abdul ya saketa sakamakon ganin ta da yai da wani, yayi kuka yayi danasanin auren ta Abban ta shima hak'uri yaita bamu, lokacin shima ya aurar da sauran yaran, itakuma tana zaune amma ba kwarjini Dawowar mu sokoto dalilin baqin cikin ganinta da yai da wani, Abokinsa Abban Fadeela sin had'u a Umrah shiyace ya dawo Sokoto Yanzu gashi munyi zaman mu lafiya, lokaci yanaja nasara da d'aukaka ta zowa Abban ki ya fito takaran governor Allah ya bashi Kowa yana k'aunar Abban ki, yaranmu suna sonki, duk da bama maganarki amma Su kina ransu, addu'arsu garemu da ke itace tayi sanadiyyar warwarewar komai, har gidan nan tazo kwanaki lokacin da hankali yazo mana Tafad'i yanda tai, itama yanzu haka tazama bata magana FUTUHATUL KHAIR ina k'aunarki, inafatan kinga ne ba laifin mu bane nak'in nemanki? Hajiya Nagode sosai wallahi na yadda ke macece ta gari, bakisan ta ba ki d'auki nauyinta har kike mata komai duk da kinsan bakida tabbas na ganin iyayenta Kinji abin da ya faru, tana magana tana share hawaye da majina, kowa kuka yake yana tsinewa Chuchu da Maman ta Allahu Akhbar nan itama FUTHA da ita kanta Maman Fadeela suka bada labarin komai, waih ansha kuka duk da FUTHA batasha wahala ba Amma dai rashin iyaye kusa da ciwo Bata fad'i rashin arxik'in da dangin Aunty Meimi suka mata ba Sosai Abban ta yace insha Allah ya d'auki alk'awarin nemosu har ita Mama NAFEE sun taka rawar gani arayuwarta Idan yai duba da yadda Kabeer da Meimi suka maida ta 'ya komai ita, to ai haka Mama Nafee itama tamaidata 'ya har school tasaka ta Bata barunta tayi aiki, tana karemata mutuncinta, tana sonta duk da ba ita ta tsince ta ba Mama kuma aisai godiya da fatan zumunci mai d'orewa, dan sunmata hallaci makaranta wadda ba 'yayan kowa suke ba ita suka sakata IMAN INTERNATIONAL SCHOOL lallai sunyi aiki Kowa dai yayi k'ok'ari akan FUTUHATUL KHAIR. Murna bata k'arewa Abban ta murnarsa tafita kowa Dangin Mamanta sunzo suma murna, daga kan Uncles da Aunties nata, sai yammata yaran Yayun Maman ta kamar su d'aya da yaran Dama tanajin larabci nan fa hira t b'alle sama sukai FUTHA na kusa da Fadeela, komai Fadeela Rayuwa tayiwa kowa dad'i, yanzu basuda matsala ta komai, sai wadda baza'a rasa ba *Bayan Sati 3* Farouq komai ya kwance masa abin tausayi, Fadeela kanta tana tausaya wa Broth nata, gashi anyi nemanta har cikin super market amma abin shiru Addu'a ita yasaka agaba, Mama taji labari itama addu'a take masa Allah ya bayyanata idan da alkhairi Yau Lagos suka tafi gidan Aunty Benaxir cousin na Abban tace, yankin Ikeja Sunje lafiya kai garin Lagos yana kyau, sun sha yawo anje beach anje unguwanni da dama Yau zasu tafi itada K'annen ta suka zo, sai wasu 'yan uwan su Dan haka itace a gaban motor anata hira tana kyalkyala dariya kanta ta juyar tana kallon gari, batason hawa flight tace gari zata gani ko a tawowar su saida suka tsaya a Kaduna nan ma tazaga Shikuma daidai lokacin fitowar sa kenan daga office zaije gida ya d'auko wasu files Cikin nishad'i yake driver nasa hira yake masa, idonsa a rufe yana hango 'Yar Makaranta da yanayinta da yaga gani lokacin da suka had'u a shopping Idonsa yake bud'e wa a hankali yana murmushi, gefen da zai kalla waih itace k'ara kalla yai wallahi itace da sauri yace driver yi sauri ka tsaya, ya zata tsayawa zasuyi amma ina saiyaga kamar ma qara speed yai na motor d'in Da sauri ya shiga da kansa yake driving d'in ya kusa kamosu 🛣 traffic 🚦ta tsayar dama gashi sun shigo wajan cunkoso duk k'ok'arinsa nayai sauri ya wuce abin yaci tura Sun wuce gashi shi mai adalci ne bayan haka ko da yazo wucewa motoci sunyi yawa Kansa ya buga a sitiyari hawaye ya fitar mai zafi, office d'in da baikoma ba kenan yafara had'a kayansa ya tawo Sokoto @ut@r h@jiy@💅🏻💁🏻 [11/10, 8:26 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [03/11 10:17 am] @ut@r h@jj@ju👱🏻‍♀✍🏻💅🏻📚📝: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussein* *Dedicated to FUTHA LUV* *Page 121-125* Tafiya tayi kyau anje lafiya andawo lafiya, sai fatan gajiya tabi lafiya Shima Farouq yazo gida lafiya sumul, koda Mama ta ganshi tasan da matsala tunda ranar aiki ce D'akin sa ta bari ya shiga, sannan ta bishi, yana kan sopa kansa yana kallon sama ya dafe kansa da hannun sa Baiji shigowan ta ba sai jin hannun Mama yai akan fuskan sa Son lafiya kana dawowa daga gaisuwa ko abinci baka ciba kazo ka fara tunani lafiya ko wajan aiki ne ko baka da lafiya? Mik'ewa yayi yana cije baki saboda kansa daya ke d'an ciwo. Mama ba awajan aiki bane. "wallahi dai inajin Mama 'yar Makaranta aljana ce indai mun had'u to saita sub'ucemun, jiya a logas nagan ta duk k'ok'arin namata magana abin yaci tura" Nakasa kuma cireta a idona, hmm Omar ba komai kuma insha Allah ba aljana bace, then kadena saka damuwa aranka Idan har matar kace wallahi saika aure ta kaji Omar Farouq d'ina gwarzo na jarumina amma awajan aiki banda wajan 'yar Makaranta Dariya ce sosai ta kama shi, yauwa katashi kayi wanka sannan kayi sallah kaci abinci sai ayi addu'a kasa nima ko har gida zata zo kaganta Murmushi yayi, sannan ya mik'e. Yadda Mama tace yayi haka yayi harda d'akko Qur'an yana karantawa Mama daga nan sai wajan Fadeela jiya namata waya bata d'aga ba, nasan fushi tayi mun tafi, tunda nad'an huce gajiya Bara naje Ai kuwa dai dan ranar da kuka tafi kamar tayi kuka, dan ma Ahmad yana nan shine fa sukaita hira harta ware Naji yana magana ma wai yasami mata a 9ja, (Ahmad d'an wan Maman FUTUHATUL KHAIR ne) Lallai Allah ya tabbatar nasan da batayi fushi ba, tuni tamun waya. Mama natafi dama already ashirye take driver ne ya fito da mota suka tafi Salamu alaikum Sis Fadeela kaina bisa wuyana nasan nayi laifi, wallahi tafiyan da sauri tazo amma amun afuwa Fitowa Fadeela tayi tana d'aure fuska tace ni ina ruwana, dama nasan haka zaki ce Wallahi ba haka ba, to kiyi hak'uri na amsa laifina kinga Mama na kallon mu kada tamana dariya Namayi dariyar, rungume juna sukai suna dariya,gaishe da Mama FUTHA tayi ta ajiye mata tsaraba. d'aki sukai sai hira, nan aka fara hiran Ahmad da soyayyan da suka fara itadai FUTHA dariya ce tata ita dai batason wata So ba, abinda sai yanzu tamasa mu bakin maganar Kai namanta broth yana gida kuma baici komai ba, couscous mukayi na zuba masa amma yakasa ci, yanata tunanin 'yar Makaranta Wace kuma 'yar Makaranta?, wa tace nan ta bata labarin tun farkon had'uwar su kawo jiya OMG! Allah sarki Allah ya bayyana ta, amma zama bacin abinci da matsala "Bara kiga namasa faten wake koda kunu ne mai zafi maybe ya iya ci Haka ta mik'e sai kitchen, wake ta d'obo agyare yake saikayan lanbu da hanta na manja tamasa sannan ta kawo alayyahu mai yawa ta zuba 30 minutes tayi tagama, sai tashin k'amshi, kunu mai kayan k'amshi ga k'amshin lemon tsami haka ta juye tasaka a tray tace Fadeela tazo sukai masa Lokacin da suka shiga yana toilet, ajiyewa sukai suka juya Allah sarki Ya Farouq wallahi yaban tausayi, Allah yasa ya iya ci, Am33n Fadeela tace Tun yana toilet yaji k'amshi yaji alamar shigowa sauri sauri yai ya fito Gurin tray d'in yayi, wow abinda yace kenan, towel ne ajikin sa ko kaya bai tsaya sawa ba, yafara zirawa kafin me? Sai flask yabari kunun ya tsiyaya shima dad'i Huum nasan FUTHA tayi shi dan wannan testing d'in food nata ne Godiya yai ga Allah kafin ya tashi ya shirya, kayan ball yasaka mai tambarin Arsenal bayanta sunan Ozil ne. bayan gida yayi, anan yafara buga kwallonsa cikin kwarewa yana nishad'i haka yaji shi bayan yaci abinci yana murna Kinga tashi muje wayan Ya Farouq ko yaci mu gani FUTHA tayi maganar, OK let's go Shiga sukai, wayam yacinye farin ciki sukayi, uhhmmm inayatafi kuma? Yana baya kwallo yake, zo muje yauwa kinsan kuwa munyi missing kwallo wallahi aitunda kika tafi banyi ba Gurin suka mik'a aikam yana wajan kallon sa sukai kaikace Christiano Ronaldo yanda sukaga yana buga ta cikin kwarewa harda kai bugawa yake FUTHA jitayi ya burgeta Bata tab'a ganin saba, amma Idan hakane yafi duk gidan kyau duk da ba fuskansa tagani bayan sa tagani, lokaci d'aya taji yanason tsayawa da saurayi kuma kalan ya Farouq A Jikin sa yaji kamar ana kallon sa, da kuzarinsa ya juya cak ya tsaya ganin *'Yar Makaranta* agabansa tazubamasa ido @ut@r h@jiy@💅🏻👱🏻‍♀ [11/10, 8:27 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [05/11 11:36 am] Last born👱🏻‍♀✍🏻💅🏻📚📝: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussein* *Dedicated to Bilkisu Sidibe FUTHA LUV* *Page 126-130* Wata d'aya akasaka badan komai ba sai don haka suke so, dama maiyayi saura indai mutum nada saurayi zaman zance duk rage lokaci ne Maman ta bataso haka ba, taso asaka ko irin 3 months d'in nan batagaji daganin 'yarta ba, amma ba halin magana saidai fatan ayi komai cikin aminci Lokaci na tafiya shikuma alokacin ne aiki yayi masa yawa kansa ta d'auki charge saboda sun gano ana shigo da miyagun abubuwa ta b'arauniyar hanya kuma da sanin staff na wajan Shiyasa yake k'ok'arin gane su waye sukeda hannu ciki, shinkafa ce Sai carton na Taliya aka shigo dasu daga Niger cikin su kaf bindogogine sai abubuwan banza Lokacin sa kad'an ne wayama sai dare suke samun yi, da rana baifi suyi 20 minutes ba suna magana FUTHA an fad'a tarkon Luv kullum cikin tsara sweetest words akeyi agayawa Ya Farouq, ga kwalliya da ake ci asha Selfie One love plx ai kasan Maiduguri koh?, eh mana ya akayi? Dama inaso kafin biki naje gidan su Aunty Meimi suma agaya musu daga nan sai sumana kwatancen gidan su Abba Kabeer Hum waye Abba Kabeer kuma ni bansan shiba kuma ba inda zaki tafiya har wani gari A'a kada muyi haka da kai, banda kamar iyayena sai Abba Kabeer sai yanzu danasami miji nagari Kada ka hanani zuwa sune jigon rayuwata sune suka ban tarbiyya sune suka koyan girki sukaban ilimin boko both of islamic Nan tabashi labarin ta kaf, tunda Fadeela data bashi labarin baiji sosai ba Nan da nan yace yi shiru to kidena kukan, yi hak'uri kifara shiri gobe zanzo sai mutafi shikenan Adena mun asaran hawaye, da ina nan saina shanye kayana amma tunda bana nan ayi shiru Dariya tai tace Allah daga gani kullu zakayi, ko fita kaji nayi kafara fad'a kenan To ai ina Kishin ki da yawa bakisan kinada qualities da ko wanne namiji ya kalleki bazai so ya d'auke Idon saba To naji kayi shiru, hhhhh to nayi tunda ankatseni, yammata na Haka sukai sallama daga nan tayiwa Fadeela da Sahaf sai Basmah yar lele aminiyarta ce sun had'u a school itama Abban ta former Senate ne, tanada kirki Basmah tana sonta shiyasa itama takeji da ita Tare tayimusu waya akan su shirya za'a Maiduguri gidan su Aunty Meimi dayake batamanta sunan Abban Aunty Meimi ba kuma yayi fice koda sun b'ata daga an fad'i sunan za'a nuna musu Mamanta tayiwa bayani sosai tayi murna tana alfahari da FUTUHATUL KHAIR yarinyace mai dogon nazari da sanin yakamata K'arfe 11 na dare yadira agarin na Sokoto duk da tarin ayyukan daya ke dashi haka ya tsallake ya bari dan bin umarnin Amarya Waya yamata ya dira yace tayi k'ok'ari su shirya before 8am dan suje da wuri,Fadeela zaiyi k'ok'arin itama ta shirya tunda yaga tana gida Basmah da Sahaf agidan suka kwana Fadeela ce take a gida Abban ta kaya super guda 10, less da Swiss ga shadda da takalma ga dangin kayan zak'i haka ya siyo yace akaimusu kafin shima Allah yabashi lokaci yaje Kayan gida biyu aka raba.d'aya dangin Meimi d'aya na Abba Kabeer, amma duk da haka saida Farouq yaqara loda wasu kayan Ita Permpers da kayan yara wajan 20 colours ta siya Mamanta tabata kud'in ga su abincin baby haka ta siya wa Babyn tasan ya girma Komai cikin tsari sukayi, Safiya nayi suka kama hanya, shida ita agaba su Fadeela agaba tafiya mai dad'i sunayi suna hiran su da murmushi kai gaskiya SO yayi Suma su Sahaf kowacce hiranta take danata saurayin daga baya aka koma chat Sudai hiran su suke yi yanayi yana juyowa wani lokacin hannu zata saka ta juyar da kansa daga kallon ta Dariya ce tasa hararen sa tayi, wow amma kinyi kyau kamar hararan tafi miki kyau k'ara muga one love Nak'i nak'ara to naji yimun labari ko kimun wak'a plx Ganin ba zatayi ba yace Idan bakiyi ba zan aje driving harsai kinsa yi oya fara inaji Huum ba yadda tai dadin ta d'aya sunyi bacci haka tafara masa wak'an larabawa tasu Maryam Haddad, Hanadi Khameel Farha yousef Salma Rasheed wow mirya mai dad'i yauwa cigaba haka tayitaimasa Daga nan tafara masa na India haka tacigaba kafin me saiganin su sukai a round na Maiduguri sun iso @ut@r h@jiy@💅🏻👸🏻 [11/10, 8:27 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [07/11 3:43 pm] @ut@r h@jiy@✍🏻💅🏻: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussein* *Dedicated to FUTHA LUV* *Page 131-135* Da tambaya suka isa unguwar basusha wata wahala ba, saboda mahaifin ta sananne ne Gida ne qato wanda ya amsa sunan sa gida a yadda tasan gidan ada yanzu anqara gyara shi an k'awatashi Da sallama suka shiga bayan sun shiga cikin gate d'in gidan manyan motors suka gani ga yara k'anana da alama taro akeyi a gidan Parlour sukai, anan sukaga kowa da kowa na gidan azaune taro ake. Juyawa zatayi saiji tayi ance FUTHA ce wallahi Aunty Jidda Sodangi tayi maganar Da sauri ta dawo Mrs Omar ce ta sakko daga kan kujera da alama ciki ne da ita dan tafiyarta ma ta canja, k'arasowa tayi har inda suke a tsaye fuskanta ta shafa tace Allahu Akhbar itace ikon Allah dama kina raye? Kan kace me parlour yacika da murna nan da nan aka shigo dasu abinci akayita jera musu da abin sha Sodangi dai itace taketa janta da hira (dama tana k'in kulatane akan kada ta aurewa Auntyn ta miji) yanzu babu dole ayi kirki Sun mata murna da farinciki da sukaji labarinta da bud'ewar bakinta da irin rayuwar da tayi cikin kasuwa da kwanan cikin dajin da tayi har komawarta wajan Maman Fadeela saida fad'a musu Kuka sosai sukasaka da suka tuno da 'yar uwarsu Mahaifin ta sun sanshi tunda Yatab'awa bawa wansu wata kwangila Wani yarone da baifi 3 years ba, yatawo yana surutu, FUTHA na ganinsa tak'ara saka kuka Abdallah ne ga kamar sa nan da Abban sa sannan kuma ga tawadar Allah a gefen fuskar sa Lallai Allah shi keda iko akan komai Ya d'aukemaka UWA, ya d'auke maka UBA ya kuma rayaka gadai misali kan Abdallah Hannun sa ta kama tace Maisunan Abba kaman tani koh? baka sanni ba Aunty FUTHA ce Dariya yaimata ya kwanto jikinta yace naganki a photo kinyi haka ya gwada yanda tayi pics d'in dariya akayi hooo Abdallah d'an rigima Munay da ragowan 'yan gidan sun nemi yafiya akan abinda suka mata, baran Aunty Nafee data tsaneta, murmushi tayi tace ba komai ya wuce sunji dad'i Kwana d'aya sika so yi, amma suka hanasu su Sahaf Basmah Fadeela anyi yawo dama gasu sarakan yawo Su dasu Sodangi da Munay suke tafiya, itakuma suna mak'ale saijan fad'a, daga yace bara yaga nan sai yace bara yatab'a hannun ta yaji wanne yafi laushi itadai hararansa take kawai Huum lallai yarinya Idan kikayi harara tafi kyau ma, amma muga Idon naki yana awani matsayin? Hannu yakai kan Idon ta yafara tab'awa sannu sannu saigashi kan hancinta zagaye yafara mata itadai ta k'ame takasa katab'us fuskarsa yakai dab da tata har sunajin hucin numfashi juna k'irjinta fat fat yake kamar wadda tayi gudun Adda Benazir tazo yimata editing lol Fuskarta ya tallab'o bakinsa zaikai kan nata da sauri ta mik'e shima haka innalillah I'm so sorry One love wallahi bada nufi nayi ba, kece Indai kina kusa dani mantawa nake da komai saike gani nake kamar daga ni Sai kene a duniyar baran wannan turaren naki Diwan Al mulkh To ainima haka nakan manta da komai, baran Idan kana mun wannan murmushin amma dai plx muna kiyaye wa kaji one love Ok Habeebaty zanyi yadda kike so, amma adena mun rowar nan k'irjinta ya nuna wai tana saka mayafi ta rife, hannun sa ta doke tace kai dai bazaka canja ba Zan canja ranar da aka kaimun ke, baran naganmu cikin jacuzzi guda munrufo bathrobe d'aya tare hooo I can't explain my Happily dat day Itadai tashi tayi tace tace kayi da wata amma bani ba, nikoh to naji amma dai inajiran ranar da zanga kina feeding ena ko Babyn mu waooo waya ga Farouq da br...... Kaga plx kabari wallahi kana sawa inajin kunyar ka, kuma ko yanzu bazan k'ara fitowa ba Haba dai One love ai fita zamuyi ma anjima, bazani ba kuma kada ka k'ara kulani tunda kai haka kake Nidai amun afawa ban k'arawa Kaji da shi, haka ta tafi cikin gidan tana murmushi mai sanyi tana k'aunar Farouq kodan irin wannan barkwancin nasa, ita yanzu yasakata jin kunyan sa wai tayi feeding nasa saikace wani baby Shima murmushi yai yanason FUTHA kodan kunyar ta, yanamata wasu abubuwa dan kawai yaga kunyarta kuma ya tsokaneta Sodangi anyi qawaye itama Sahaf anyi k'awa. Abdallah dai ya mak'alewa FUTHA ko'ina zata yana wajan, yanzu ma kuka yake ganin tafiya zasuyi su barshi anyi anyi yayi shiru yak'i Mr Omar itace tace to sutafi dashi (tazo ne saboda yaron da akayi, amma a katsina take Sodangi tana wajan ta). Haka akayi kayansa suka had'o masa itama tai murna da aka batashi batada abinda zata sakawa da iyayensa Sai addu'a sun nunamata gata da kulawa Haka motar su taja, suna d'aga wa juna hannu har ta k'ule Hira suke akan karamcin da aka nuna musu da karammawa da aka musu.Har suka kawo Sokoto daga nan suka d'auki hanya sai gidan su Abba Kabeer Hajiyan sa tayi murna tagje kuka anan tabasu labarin neman ta da sukayi ba'a same ta ba, 'yan uwansa suma sunzo kowa ta tayata murna daganin iyayenta da tayi, baran da sukaji itad'in Waye uban ta Kwana d'aya sukai, Abdallah yasan su sosai amma wannan karan fuska yayi akan kada a d'auke shi ko arabashi da Aunty, sudai dariya sukai Hajiya tace lallai Yaro kasan watayi rainon ka ta taimaki mamanka da cikin ka, FUTHA alkhairi ce awajan ka kaima Eh Hajiya saikace yaji mai aka ce haka nan ma suka baro tareda abin arzik'i da kukan rabuwa Dangin Abba Kabeer sun nunamata k'auna sin sota, sunkuma karemata mutuncin ta *Bayan sati d'aya da dawowar su* Adaidai wannan lokacin ne suke rabon goro, duk inda zata da Abdallah take zuwa shima baya yadda da kowa, daga ita zai uncle Omar kenan Gyaran jiki ake mata, shiyasa kwana 4 kenan su Fadeela sune akan rabon, danginta sun fara zuwa gid yafara cika Da wanda suka santa da wanda basu santaba yanzu sun ganta kusan kuka takeyi Idan taga yawan dangin ta gasu Sodangi sun mata waya suma jibi suna hanya Oga dai ya koma aiki yasa shi gaba, dole sairan Friday zaizo shida tawagar abokansa @ut@r h@jiy@🏃🏻‍♀💅🏻 [11/10, 8:27 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [08/11 9:41 am] @ut@r h@jiy@✍🏻💅🏻: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussein* *Dedicated to FUTHA LUV* *Page 136-149* Amarya tayi tsaf gyaran jiki ake mata wanda ya fiddo da tsantsan kyau da hasken ta, batada damuwa ko d'aya saita rashin abokin tsokana kusa. Duk da kullum suna mak'ale q waya, amma sosai suka jigata da rashin juna baran d'an kwanakin da sukayi tare sunyi shak'uwa Dangi an had'u, yan katsina duk sunzo wasu gidan Hajiya suka sauka, Aunty Meenah itama da nata tawagar da yaranta da jikokinta biyu na wajan 'yarta duk suna zo Dayake lokacin kad'an suka saka, sai Yau aka kawo lefe akwati two set, sai sark'an English gold data Gold k'iran Dubai tareda awarwaron su Sai 100k acikin kayan, shinkafa buhu6, gero 6 Sugar shima haka buhu 6, sai chewing gum carton 6, komai yayi ba k'arya Idan ma akwai da kud'in yin ne Dangin Aunty Meimi kamar gori kusan duk yammatan Sai da suka zo Sodangi itace kan gaba Fadeela itama tanad'an mutsikka abubuwan gyaran jiki itama tai kyau, angama komai da ake buk'ata A Yau Thursday akayi Igbo Day a harabar gidan su akayi, Ango baizo ba sai gobe dama mata ne zallah saboda shigar da sukayi exactly Igbo girl sunji dad'i ma dabaya gari Abban su yayi musu order na kayan, so duk wanda yazo Idan ya cancanta sai abashi, kafin ranar and'anyi rihaza akan yadda rawar zata Kaya Ko da aka gama aka watse yammata sallah da wanka sukayi, itadai bacci tayi, su kuma chat aka hau (kamar Auta tanason zuwa wani waje babu mai hanata chat) Friday Ango yazo nan ma anyi Lunch maikyau da k'ayatarwa a NAGARTA multipurpose Hol anan akayi Amarya shigan Material yellow tayi sai head da takalmi blue tayi kyau, Ango kansa yasan yes ce amaryar tasa Washe gari Abuja suka tafi, Uban gidansa ya had'a masa dinner a Sharaton Hotel inda daga amarya har Angon Kakin Custom suka saka shida abokan sa, kyau dai koban fad'a ba kunsan za'ayi Light make up Fateema Ta Annabi tamata, gashin ta yasha gyara guri guda aka ajiye shi mata shi, sai wani net maikyau tayafa asaman kayan sai takalmi da jaka colourn kayan tayi kyau Save Ur self ne awajan, nan naga K'ungiya ta writers kowacce ta d'ebo abinci cikin plates ga nama ga chicken paper da chicken noodle ga juice kowacce ba magana sai zirawa take cikin gayu taunarma a hankali Gayu nace dole kuja aji Daga baya naji wani k'amshi na tashi azuciyata nace wace wannan haka, meimi bee tace Auta Kwaiseh ce yar garin mu, wow ashedai writers ganin su yafi jinsu Baran danaga Maman Bobo, STYLICH, Ya Hajja Queen Meemi Jabo Nafeesa Anker, Aunty Lubie itada Amaah kai Lallai writers yan gayu ne ga Faty malunfashi wai carkwad'i kowacce taci gayunta tana tafiya da cin abinci cikin nutsuwa Ni gefe naja ina kallon su, shigowar wasu su biyu itace ta tsaidani da abinda nake. Kai Jidda Ja'o dama zakizo? Nazata baku gama presentation d'in ba? Wallahi bamu gama ba, inason zuwa dai maganarta mai sanyi, a d'an sauri itada Rookie Sadau ne Anan suka zauna kowacce tafara hiran school da exams ko test da zasuyi, Anee banganta ba inji Feedoh yar ficika, eh tana exam itada Amrah Ok Allah yabada sa'a, ansha rawa da kid'a anyi selfie writers ansha photo na tarihi da selfie stick Taro an tashi lafiya, amarya Ango yaso su kwana amma tak'i adaren suka biyo flight suka dawo Biki daidai gwargwado anyi shi cikin ni'ima da k'ayatuwa Maman Ango itakanta wannan shine bikinta na farko bajinta daidai anyi, ankashe kud'i dama akwai su Tare sukai mothers day, da Maman FUTHA tunda kusan k'awayen d'aya, Ango da amarya nan ma sunje *Yau ranar Lahadi 10:00 aka d'aura auren Fadeela Abdallah da zakaran mijinta Omar Farouq Ahmad*akan sadaki mafi k'aranci 50k saboda neman albarka [08/11 12:15 pm] @ut@r h@jiy@✍🏻💅🏻: Amarya tayi kyau, Gexna tasaka wadda kayiwa stone work, ajiki have gown ce make up maikyau, ga danginta baibaye da ita Marok'a sunsamu abinyi, Abdallah yana mak'ale da ita Taro dai anyishi cikin lafiya amarya ankaita gidanta dake kusa da gidan iyayen mijin ta. Wajan Mama aka fara kaita, fad'a akamata na tsakani da Allah Abbanta saida yai hawaye yanason FUTHA kodan ladabin ta Bayan kukan rabuwa da gida da tayi, da kuma kukan rabata da Abdallah da akayi harta tawo tanajin kukan sa, kan saiya bita Gidanta plat house ne, gidane ko cikin Maitama Sai haka, iyayenta sunmata abin arziqi da bajinta koina cike yake da Kaya gadonta biyu komai dai biyu akamata ga gara da aka kaita da ita K'annenta hardasu aka kawota, kuka take sosai, jin yadda siketa tsokanar ta gasu Sodangi sunce gobe zasu juya kuma harda Abdallah abin biyu ya hade mata ga zafin rabuwa da iyaye gana Abdallah Fadeela da Sahaf suma shak'iyanci suke mata akan yau za'ayi wuju wuju da wata, Lallai broth namasa murna zai kwashi gara irin wannan gyara da kika sha haka waih broth zai jishi daam Kada dai ki rikitamana Yaya ehe, kwashewa sukai da dariya Basu suka tafi ba saida Ango yazo shi kad'ai yazo batare da kowa ba, turus yai ganin su Fadeela Ku mekuke yi?, dama kira muke kazo sai mu tafi kada abarta ita d'aya. Ok a tashi to Haka suka mik'e kowacce tana k'unshe dariya Suna fita ya haye gadon yana murmushi one love sun takuramiki da magana koh? Itadai shiru tai. Lek'a fuskanta yai data ke k'unshe cikin Maroon lifaya Kai one love me kikayi idonki yayi ja haka, ko duk kukan ne? Kai ta kad'a OK, bakison akawoki gida ne shiyasa kike kuka, yan kaki zanyi ko cin naman ki zanyi, tab'a jikin ta yai, OMG Plx kidena kukan haka jikin ki yayi zafi Plx abage kiyi shiru Haka yayita lallab'ata harta ware jikin sa ya d'orata lifayan yafara warwarewa mata acewar sa akwai zafi Da wayo da dabara sai ganinta tai !! waih rigar dake cikima ya cire kanta ta cusa da k'irjin sa tace plx one love meyasa kalli kaga kasaka ni jin kunyarka kuma ai nibanjin zafi Tana magana a shagwab'e,dariya yai yace to ai inajin zafi nidai oya tashi nasaka miki rigarki muyi alwala muyi sallah ga almara'i da cocktai na tawo miki dashi Yauwa tashi kare jikinta tafara shikuma yana k'ara sata jin kunyar sa ©@ut@r h@jiy@💅🏻 [11/10, 8:27 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [08/11 1:37 pm] @ut@r h@jiy@✍🏻💅🏻: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussein* *Dedicated to FUTHA LUV* *page 141-145* Hanyar toilet yayi da ita, shiga zatayi taga shima yana k'ok'arin shiga tsayawa tai, Malam yah? Shiga zanyi bansan ki wahalarmun da hannun ki naki wajan cud'a jikin ki, kibari na yimiki wankan aishine soyayyar koh? A'a ba haka ne ba kabarni nayi wanka sannan kaima ka shiga, amma ai.... Amma ai me? Nidai dan Allah kabari, nidai dan Allah kabaaari maganarta ya kwaikwaya kana ya juya ya koma beside na door d'in Kai ta juya azuciyar ta tace wannan mutum haka, lallai na bani Wanka da alwala tai, tana fitowa ya taso oyoyo one love bara ashafa mai asaka powder koh?, wayacemaka ana saka powder Idan za'ayi bacci? Ba kowa to kawo natayaki shafa humran nasan dole Sai ansaka kodan arikitani Huum, nifa wallahi kanaban dariya amma zan rama wataran Eh naji ki rama, kunya ba irin wadda bataji ba, lokacin daya warware towel d'in jikinta mai ya shafamata baimata komai ba, saidayaga yashiryata sannan shima tashiga toilet d'in Dadduma ta shinfid'a zama tai akai tafara lazimi, tana rok'on Allah yabata juriya yaimata lamuni dayara nagari ya saka albarkaa auranta Kodaya fito shima gabanta ya tsaya bayan yasaka jallabiya fara, Sallah ya jasu raka'a biyu addu'a yayi masu zafi kana suka shafa Anan inda suke nan yazube kayan abincin tareda fruits masu sanyi a yan yanke, kamar tak'i ci amma dolen ta ta ci, shine yabata harsuka gama Brush tai shima haka, k'aramar Riga tasaka sannan ta d'ora zani akai tace masa asubah tagari bacci yaci k'arfina kasan kwana wajan biyu banyi bacci ba Tana gama fad'a ta juya, murmushi yai yace yarinya zaki gane yau d'in ma ba bacci dan sai gentle ta wasa jinin ta Kamalla komai yai kan system, da kansa ya fita ya kashe kayan electrics ya tofe ko'ina da addu'a before yaje shima ya kwanta Kan gadon ya haye, a hankali yafara shafata yanamata waiwaye cikin kunne, juyi tayi tacigaba da baccin ta, harshensa yasaka cikin kunnenta, Huum Plx one love kabari inajin bacci Ohps baby ba abinda zan miki I just want to play fa kawai Bakinsa yasaka cikin nata wani irin hot kiss yafara bata tun tana gyagyad'i tana mayen bacci harta ware, jikinta lumus yai tanajinsa Hannun ta yasaka a k'irjinsa magana yai bansan mai yace ba, naga dai tana wasa da wajan ahaka suka d'auki lokaci daga baya ya rungumeta suka lula bacci bayan yarabata da kayan jikin ta Da Asubah shine yafara tashi, murmushi yai tace sleeping beauty, kanta yashafa yashiga alwala yai Ita bata tashi ba, ya kyaleta ganin da lokaci kuma yasan ta gaji koda safe tayi 8:45 ta farka agigice hasbullahu wa ni'imal wakheel, Ya Farouq baitasheni ba why?, gefenta takai idonta a kwance yake akan sopa da carji a hannun sa A hankali ta mik'e bayan data fuskanci ba komi jikinta, wanka da alwala tai a had'e Atamfa tasaka amaryarta sak, bai motsaba harta idar da kwalliya da Sallah, fita tai tafara zagaye gidan kai yayi kyau kujerunta Royal ne d'ayan kuma normal kujerune dining mai 6 dame 4 Waje tayi anan taga garden amma arufe yake bud'ewa tayi, flowers different colours gasu nan Lokacin daya farka baiganta ba hakan yasa yai sauri ya shirya ya biyota inda yake jin motsin Rufemata ido yayi yace meyasa baki tashan ba kika yi wankan ki ke d'aya? To ai bacci kake kuma Bansan tashin ka amma next time zan tasheta OK baby na Dashi da ita suka zagaye gidan komai irin yadda suke so ne, daga gidan Mama aka kamusu breakfast, harda Roman kaza Sai k'amahi takeyi [08/11 1:57 pm] @ut@r h@jiy@✍🏻💅🏻: Huum, yarinya nizanci wannan kazar tunda ke ai baki yadda anyi abinda zakici ba Naji kacinye ba komai, ta lura magana yake son janta da ita, inason matata amma ita tana k'ina haka dama rayuwa take Dariya ce ta kamata jin wai waqa yake a haka, Lallai one love bata kyauta ba ana sonta tana k'in mutum kai gaskiya tayi rashin kirki Haka sukaita zolayar junan su aure da dad'i Sai wajan yamma akazo mata sallama danginta dasu fido Sodangi, ansha kuka Abdallah dai yak'i binsu har kusan suma yayi akan anshigar dashi motor, bashiri suka direshi anan suka musu fatan alkhairi Sodangi tace Yaro wato Auntyn ka kasani zamu rama ne Fadeela sun shigo bayan tafiyar su, girki sukai anayi ana shak'iyanci suna yasukaga bata tafiyar tata ta ko suga alamun tasha kuka, kodai ba'ayi abin ba Uwaku mai za'ayi kinga Fadeela dama haka kike, tashi bazaku lalatamun mata ba Ku fice, sunabm dariya kowacce cikin kunya yakamasu suna irin nan zancen suka fita, Abdallah binsu yai yasaba da Fadeela dama Huum kinji yaran nan koh, Allah ya kyauta Zaman su zamane na gaskiya da amana da mutun ta juna, sun sake da juna shi kuma ya baje yana kwasar gara ta abinci da abin sha Yau watan su guda kenan ya barta ta sake dashi amma bawai dan wani abu ba, kuma gashi hutunsa ya kusan k'arewa shiyasa yau za'ayi final ba semi final ba Da confidence nasa yashiga gida, tarbonsa tai kamar yadda take yi, d'aga ta sama yai yace yarinya taqi tayi k'iba kodan ban bata white milk ba, amma I'm sorry yau zaki santa Huum Baby mene kuma naji ka fad'a yanzu?, Huum zaki sanine yanzu dai wanka abinci shine gaba nayi sallolina Saving nashi tai, tare suka ci coconut rice ce sai stew, sai lemon pineapple datayi masa Kai abincin yau yayi dad'i, kamar kada na k'oshi tanajin dad'i Idan yana yaba abincin ta, wataran shima yanayine saboda yana ganin murmushi akan fuskanta burinsa yasaka ta farin ciki Wanka ya shiga, abinci yafara ci, kodaya fito k'in kallo yabari ayi, yace ta tawo tamasa massages ya gaji Bata kawo komai ba, tace 5 minutes narage kayan Jikina, haka tafara masa yana lumshe ido yana bud'ewa tana masa hira mai dad'i Daga massages kuma naga abin yana neman wuce gona iri ba shiri na tarkata kayana da wayata da charger ta nayi gaba @ut@r h@jiy@ [11/10, 8:27 PM] ‪+234 809 308 3613‬: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussein* *Dedicated to FUTHA LUV* *page 146-150* Sad'af nayi gaba abina nahau online naga me NWA gidan hira suke nasan ana can ana shafta ina shiga kuwa da Idon Jabo nafara tozali ta bazo shi Aunty Sady kuma ta watsamata barkono dariya aka saka Anan na shan take daga nan bacci yafara d'iba na ana nayi a parlour amma wani ikon Allah komai cikin gentle banji kwarototo ba ko wani hatsaniya ko kuka Sai da akayi assalatu na koma nasan dai komai ake angama baza'ayi second round ba Leqawa nayi lah ikon Allah bacci naga sunayi, itada shi amma bedsheet d'in bana farko bane, har blanket d'in ma saukar numfashi naji a hankali waih ai ina lek'a Idon FUTHA naga ya kumbura daga gani ansha kuka anyi gwagwarmaya afilin daga, gentle ta wasa jini Bacci dai take suna k'ank'ame da juna, kamar za'a kwaceta a wajan sa So mai dad'i da tsafta shine yake wakana awanan gida kowa yazo sai sun bashi sha'awa tana girma mashi tana bashi kulawa tana kula da cikin sa da gado kuma Lallai kayi dace da mace ko miji nagari shine ka more kuma kasan ribar aure House gal da aka bata, aikinta shara wanke wanke mopping amma ko kwanon da maigidan zaici abinci Bata bari ta tab'a, abinci kullum Idan tayi saita kaiwa Mama wataran gidan su ma tana kaiwa Iyayen suna alfahari da ita Fadeela itama ansaka rana, Mama bata tab'a zuwa ba saiyau datazo itada Maman FUTHA Murna inataka saka ina taka ajiye wa, komai d'akko musu tayi wani abin dariya a freeing tattasaine adafe shima d'akko wa tai sudai murmushi suke ganin yadda 'yarsu tayi kyau Lokacin daya dawo shima yai murna, tareda Abdallah sukazo FUTHA taso ya zauna amma yak'i shidai Maman Fadeela itace tasa yanzu itama Fadeelan yamata yaji Iyayen ta maza suma sunzo qawayenta kowa sai tabashi sha'awa Mijinta yana kula da ita, tare suke aikin gida, ayi ball tare ayi wanka komai tare Idan akazo 'yar Lido Idan taci kansa take fad'awa tana looser looser daga wannan wasan kuma zai birkitota tashiga faranta ran juna FUTHA na k'ok'arin akan mijin ta, tana kyauta tamasa sosai *Bayan 5 months* Sun koma Lagos dan har addmition ya nemamata LASU, tana karantar Micro biology, tana qoqari akan karatun ta, chat da wani abu duk ta ajiyeshi gefe, burinta kawai tayiwa mijinta abinda zaiyi alfahari da ita Sai karatun ta data saka a gaba Farkon dawowar su ta hadu da Mama Nafee a Lagos ba k'aramar murna sukai ba, anan tagayamata tadawo nan da saida abinci tabaro garin su Kud'i suka bata mai yawa, Abban ta dayaji labari gida ya siyamata maikyau yasa aka kafamata runfa anan take sana'arta Lallai taimako yajamata riba babba, itama tanawa FUTHA abin k'aruwa irin na garin su, kuma tana kula da ita sosai Su Musa yaran Mama Nafee da suka taimakawa FUTHA suma sun dawo Lagos Mijinta yana k'aunar ta super market ya bud'e masu anan cikin Agege FUTHA Allah baibata ciki ba, har yanzu basu damu ba ada ya fara tunanin ko karatun datake ne yasaka ta yin wani abu, amma daga baya yagane Allah ne bai kawo ba To Sai muyi fatan Allah ya kawo nagari ba saurin haihuwar ba @ut@r h@jiy@💅🏻✍ [11/10, 8:27 PM] ‪+234 809 308 3613‬: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussein* *Dedicated to My Besty Nafeesat Anker Allah yaqara lafiya. Ameen* *Page 151-155* Lokaci yana tafiya rayuwa na juyawa komai na Allah yanada iyakarsa, gashi yanzu lokacin bikin Fadeela ne yazo shiri suke zasu koma Sokoto Allah ya taimaketa sun sami hutu a lokacin Tun safe take yin shirin ta na tafiya tana jiran sa amma shiru, Har wajan 4 pm bai dawo ba sai yanzu dataji k'aran bud'e gate Assalamu alaikum One love amun afuwa aiki yamun yawa sosai, amma gashi na dawo Yana magana yana shigowa, tana kan kujera ko kallon sa batayi ba, ta gane sa bayason fita ko'ina shiyasa daga school sai wajan Saloon ko k'unshi bata zuwa saidai mai k'unshin tazo Wata k'awarta tayimata hanyar Mai kitso da k'unshi Asy Khaleel tana Lagos Haba yammata keda Idan mukaje two weeks zamuyi natsaya shirya komai fah shiyasa Ai haka zakace indai fitace yanzu zaka fara cewa wani abu, tana magana bakinta yana turo wa, OK naji amin afuwa ko nasami relief Dariya tai ganin yana neman kamata tasan kwanan zancen kafin me daga ita harshi sun shan take daga nan kuma sai Oga Master room Tafiya tasha ruwa dan koda suka kamalla abubuwan su, suna mak'ale da juna bayan sun fito daga wanka Hira suke akan karatun ta, yanamata tambaya tana bashi answer akan cikin sa take tana d'an wasa da sajen sa One love yes One love yah?, nace maizahana muje Asibiti kaga har yanzu shiru wajan one year da rabi da auren mu, kaga kuma wasu 9 month ma sun haihu Plx I beg muje ko wata matsalan ne Birkitito yai, k'ara matseta yai ajikin sa, yace FUTHA Allah shine yakeda ikon komai, kuma Idan yaso ayanzu ma yabamu nasaka kwaina ajikin ki, Idan kuma baiyi nufin haka ba wallahi ko zamuje ko'ina akan Haihuwa Bazamu samu ba, aibamuyi jimawar dazamu fara zarya wajan likita ba Kuma Idan kinyi tunani Maman ku tayi wajan 3 years kafin ta haifeki, batak'ara Haihuwa ba saibayan 9 years lokacin da kika b'ata Maman mu saidata jima kafin nima ta haifan data haifan Sai Fadeela daga kanta bata k'ara ba Kinga kuma yanzu sai labari tunda gashi sun haihun mune yaran na su, so Kada ki k'arasa maganar zuwa wajan Doctor kinji? Insha Allah haka suka manta zancen suka shiga sabgar su Washe gari flight suka bi sai Sokoto garin ziyara Gidan su suka sauka saida suka huta ma sannan suka shiga gidan, waih ina zansakaki Mama nan tai tayi dasu, dangin ta sunzo kowa sai yabon alkhirin FUTHA yake dayake wasu sunje wasu kuma Idan sukazo suna zuwar musu Da daddare gidan su taje, k'annen ta kamar sa cinye ta saboda murnasu, Abban ta yaji dadin ganin ta cikin kwanciyar hankali batada damuwa Maman ta ma haka, sai wajan 12 yazo suka tafi, Biki anyi shi cikin kwanciyar hankali da lumana amarya tayi kyau anyi dinner kala kala Ango yasha kyau Libiya aka kaita inda Ahmad yake tunda acan komai nasa yake, cousin d'in FUTHA ne, so ita ta lulaqa dangin Mama aka kaita Mutane masu karamci da sanin Yakama ta, da mutunta juna, Fadeela ansha kuka dama akace aure yak'in Mata mai d'auke mace daga cikin gidan su, unguwar su area tasu, garin su watama k'asar su kacokan Allah kaimana mai kyau One weeks sukayi a Libiya aka juyo, akabar kowa da halinsa Fadeela dai kowa yasan tanada kirki, su Sodangi duk sunzo zumunci sosai suke Abdallah dai ikon Allah Fadeela itama yak'i ta dole dai FUTHA itace ta d'auke shi Mijin ta yanason Abdallah sosai, baran yaran mai hankali ne, haka suka tarkato suka dawo gida. Sati d'aya suka k'ara suka koma gida, Maman Fadeela kullum addu'a tata Allah yabawa FUTHA ciki mai albarka itama Maman ta haka Hajiya kakar ta itama burinta haka, baran Abban ta shi har sawa yayi ataimaka da addu'a Allah dai ba'aimasa tilas sai ran da yaso *3 years Later* FUTHA ta k'are karatun ta cikin nasara da sa'a service ma take yi, Allah ya taimaketa a kusa take yi wata ma'aikata ce Amma duk da haka ma bata zuwa sosai, Farouq yak'ara samun matsayi awajen aikin sa rayuwa tayi musu dad'i Yazama chief na custom duka, gida aka bashi ga securities da aka bashi motoci ma wajan 3 aka bashi, gidane babba part wajan 3 ne agidan Anyi walima tagani ta fad'a, FUTHA tak'ara girma tayi kyau rayuwarta ta inganta Abdallah yazama saurayi, yanzu haka ma yana dangin Abban sa ta kaishi yagan su Fadeela ta haihu ansamu mace FUTUHATUL KHAIR aka saka mata yarinya tayi goshi ta d'auko farin jinin mai sunan ta Yau dukkan su suna Sokoto ana taron family, ita tarigashi zuwa shi sai aranar yazo tunda komai ya canja yanzu Tun tawowarta takejin ba dad'i amma haka ta daure, ga kasala da bacci datake Ji tun suna gida wataran kafin ya dawo ma tayi bacci Ko hira ake kan kace me bacci ya tafi da ita, shiyasa yake cemata lazy yanzu tayi wajan 2 months ahaka amma kwanan nan tafijin kasala Maman sa ta lura da ita da yanayin ta, hakan yasa tace bara dai agama taron suje Asibiti ko zaton ta ne yake son tabbata Lokacin dayazo bacci take, shiyasa basu had'u ba, sai a wajan taron Jinjina ta kaimasa tana murmushi, shima haka tunda wajan maza daban, sosai taron ya k'ayatar aka d'anyi abubuwa da dama aka k'ara sanin wasu dangin na Abban su Farouq Anci an sha anyi pictures sosai anyi musayar number ta waya, amma fa FUTHA ita bazata ce ga abinda akayi ba, dan rabi baccin ta tasha har taro ya watse Basu zarce gida ba, saida Mama tace aje Asibiti aga maiyake damunta, badan taso ba akaje tunda ita bacci yaci k'arfin ta Alhamdulillah Allah maibawa mutum abinda yake so lokacin da baiyi tsammani ba, gwajin farko saiga ciki wata uku wayyo murna farin ciki Ko kafin su koma gida labari ya bazu, Abbanta murna zaiyi jika k'annenta ma haka Badan Mama taso ba tabashi matar sa suka koma amma saidayasha kashedi akan ya kula da ita Komai take so yamata, akan lokaci shidai to yake cewa shida yafi kowa murna akan cikin amma shi akewa takara Haka suka koma, suna rainon cikin su babu laulayi sai bacci, shima ya ragu yanzu, Mama Nafee itace kullum take kamata abinci saboda nata take so Tafi tafi cikinta sai girma yake, duk bayan one to two weeks ake zuwa Asibiti, kuma Mama na waya akan lokaci taji ya jikin nata Cikinta ya shiga watan haihuwa, shiyasa Mama da kanta tazo ta d'auketa kada ta haihu ita d'aya Shima haka yaso, saboda aikin sa, gida kuma duk da da mutane amma dai gara tana kusa da gida Kayan baby kamar Hauka aka siyo, komai dai sai san barka, ba k'arya akwatu set akayi ma baby kafin ma yazo ko tazo duniya @ut@r h@jiy@ Loading Second to d last episode......... [11/10, 8:27 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [10/11 7:58 am] @ut@r h@jiy@✍🏻💅🏻: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussein* *Dedicated to FUTHA LUV* *page 156-160* Alhamdulillah kulawa dai dai gwargwado tana samu wajan Mama Bata barinta ita d'aya koina ta zauna Mama na wajan Daga Asibiti kullum Sai an turo wata nurse ta kara duba lafiyar ta Zaman gidan yamata dad'i, batada matsala Abdallah ya dawo fitina salamu alaikum, Mama tare suke kwana saboda Abba yaje umrah shiyasa Tare a gado d'aya suke bajewa Daga gidan su kullum sai an kamata abinci, k'annenta kowa rige rigen zuwa dubata yake Farouq yanamata waya akai akai, kullum burinsa Allah ya sauki Matarsa lafiya 4:30 dai dai na asubah FUTHA ce zaune kan dadduma bayan ta idar da nafeelfun ta carbi take ja, har akayi Assalatu tana kan dadduma Mama itama ta tashi lokacin Tashin da zatayi danyin raka'atul fijr, habawa gaba d'aya mararta ta rik'e takasa katab'us haka Mama ta fito ta tarar da ita Yan aikin gidan ta kirawo bayan taiwa driver waya kan ya fito da motor Allah sarki har suka isa asibitin tanata mirk'ususu, sai yada kai take, tana yarfe hannu hawaye wani yanabin wani A haka suka k'arasa da gudu aka d'auketa sai labour room, Haihuwa ce amma kuma lokacin baiyi ba, gashi wahala take Idan tayi nan saitayi nan Har 7:00 ana abu d'aya ita takasa gayawa kowa ma, addu'a takemata sosai itama FUTUHATUL KHAIR bakinta salati da hailala yake yi ba wannan ihun da kwakwazo irin na sauran Mata Shikuma acan kaida 8 yake mata waya, ya buga shiru har ba adadi jikinsa yabashi wani iri tun asubah daya farka Jin ba'ayi picking ba gata Mama ya buga hakan yasa bashiri yaje office yai signing wasu takarddu yabiyo flight 10 dai dai awanann lokacin ta wahala ta jigata ita kuma Haihuwa tazo, gashi bata da wani k'arfin Iya komai Allah cikin ikon sa kafin ma afaramata wasu abubuwan faya ta fashe cikin mintina k'alilan ta haifo Babyn ta Namiji k'ato tareda mabiyya suka fad'o Adaidai nan ya shigo asibitin shima bayan bayanin daya amsa wajan yaran gidan su lokacin daya je Yaro tabarkalllah an gyarashi an shafeshi da zaitun angoge sai bayan 4 hours kuma ayi wanka Reception ya shiga nan yaga Mama a zaune da sauri ya k'arasa Mama yayah? Bayani tamasa kafin yace komai, ankawo baby cikin farin shawl yaci fararen kayan sanyi ga gashin sa a kwance duk ya cika fuskar sa K'aidar asibitin sune zasuyi maka komai, har maijegon su zasu bata kaya da pad bill shine dai zaiyi aiki Masha Allah abinda yafito abakin su lokacin da suka amshi babyn, yana hannun su duka yaro k'ato dashi Waya suka bugawa gidan su FUTHA, kafin wani lokacin sun cika asibitin yan uwansu duk sunzo Hajiyan su itama saigata dayake anmata waya Maman FUTHA tazo da tayi kamar bazata ba saboda kunya, tunani tai abin aina farin ciki ne, kuma futha dai ba ita tayi rainon taba bare ace da kunya mayafi ta yafa, shine fa ta tawo Yan Asibiti da staffs kowa ma yasha kyauta kud'i kujeran Makkah haka sukabada biyar da wadda taka musu baby da wadda ta amsheta lokacin da aka kata, da wadda tayi jigila da ita tana lobour room haka yabisu da kujeran Makka Basu suka baro asibitin ba sai wajan 2:00 ta farka taga dangi da yawa ga baby, bata karb'eshi ba ganin da mutane Tarkatawa sukai akayi gidan Mama anan za'ayi jegon tunda anan aka fara rainon cikin Har kawo Haihuwar sa Abdallah anyi k'ani yana kusa dashi kamr ya cinye saboda murna Maman FUTHA daga Asibiti ta zarce gidan ta Hajiya ce ta biyo su itace zatayi wanka tunda anzama d'aya Mama ta d'auki Hajiya kamar uwar mijinta Angon k'arni dai yakasa fita daga ya ajiye baby zaizo yak'ara d'auka, abin dariya ma Ruwa aka d'ora bayan ansiyo kayan cikin garwa, yana zafi baby aka fara yiwa kafin Uwar Anyi daru wajan wanka dan ita kuka tasaka lokacin da Hajiya tace tashiga ruwa, gani tayi kamar ma tafasa yake cikin sa, ba yadda ta iya tanaji tana gani ta dannata da k'arfi Da zafi amma ana yan mintuna saitaji dad'i harwani lumshe ido takeyi, bacci yana so yatafi da ita Kya taso ai da kuka kika saka, yanzu kinfara jin gatan da ake miki shine zakiyi bacci, huum wani gata kindai azabtar dani wallahi gara Haihuwa da wankan Indai hakane, ni ko ihu banyi ba amma wannan ruwan kina zuban shi ihu nasaka Kyaji dashi haka suke fito ana fad'a dariya yan d'akin suka ringa yi Fadeela ana mata waya, dama ita a ready take, tunda taji ta koma gida, murna tai tace a turo mata photon babyn kafin suzo dan yau ko gobe zasu ganta Kafin dare kowa yaji Haihuwar k'awayen ta wasu sunzo ma, na Lagos duk sunji Kowa murna yake mata, mijinta dai bak'i sun hanashi sakat, daga ya shiga mutane zasu fara sallama Shi yana so suyi magana me take so, dan da safe yake son komawa Dole sai hak'uri yai da asubah ya shiga, nan Mama tace yabari Fadeela dasu Basmah suzo ayimasa waya Idan suka lissafa Ok Mama nabar ayyuka, zan koma sallama yai musu Ji yake kamar ya tafi da Babyn tare da uwar y had'a yaringa d'aukan pics harsaida mama tace ya isa Nan ma saidayace kullum aringa d'aukan pics na Babyn aturo masa Tom za'a turo, ba kunya ita Uwar ma hartafika jin nauyin mutane, amma agabana kake wannan maganar Kansa ya shafa yana murmushi yayi wa FUTHA peck a kumatu yai saurin fita yabarta dajin kunyay Dariya Hajiya tai tace ga k'arshen kunya ya nuna Kaya nagani na fad'a kakannin yaro suka masa, da suka dawo daga Saudi, kowa kuma burinsa yai musu abin bajinta jikokin su na farko kaya har kusan rasa inda zata saka tai Fadeela dasu Sodangi Basmah Sahaf Stylich Munay Mrs Omar Aunty Nafee Aunty Jidda dukkansu sunzo yanzu sunzama kamar yan cikin gida Tare dasu akayi lissafin komai da abubuwan rabo duka dasu akayi A account d'in Stylich aka saka kud'in ma, kayan flour dasu lemo Abban FUTHA yace suje Hotel Su karb'a yayi magana Yaro yazo da goshi, Kayan snacks duk Abban tane ya d'auki nauyin da lemo da ruwa A gida suka ce za'ayi ba wata fita da za'ai, komai cikin tsari akeyin sa da gwanan cewa Gobe ne suna, gida yacika ya tunbatsa da mutane yammatan dasu Fadeela gidan FUTHA suka Shiga itama anan ta zauna aka mata k'unshi ja da bak'i Anan kuma suka ajiye komai da komai nasu, Har kayan sawar su danata Abdallah yaga yan uwa cikin su yashiga tunda yasan wasu Ango tun asubah yabiyo jirgi yazo, yace dashi za'ayi sunan Yaro yaci sunan Muhammad Ahmad, za ana cemasa Sultan haka suka tsara Taron suna anfara cikin nasara ba kace nace ba hayaniya abinci ne kowa yaci yakuma ya tafi da shi anyi hotuna na tarihi kowa kagani cikin annashuwa yake Dangin Maman FUTHA gidan ta suka sauka, wasu kuma suna gidan su, Babyn aka kai musu ya jima itama daga k'arshe Farouq d'aukan ta yai yace taje ayi photo da ita tunda danginta suna can Taji dad'i sosai, suna ya qayatu FUTHA tasha kayan barka sosai writers da basa bada komai sai dai aci a tashi wannan karan sun bada dan ya Hajja turmin Super ta bada Nafee Anker kuma set na overall guda biyu, Queen Meemi ita 5000k ta bada sunyi k'ok'ari sosai dai wannan karan FUTHA tayi kyau, tasaka kaya masu kyau, daga super sai Swiss sai Sanata da Sharaton tayi kyau sosai Fadeela matayi kyau, Abdallah shima kaya wajan set goma akayi masa banda wanda Fadeela ta kamasa tunda d'an gidan tane kai kowa a wajan ya fidda tsantsan kyau nasa Taro ya tashi lafiya sai fatan Allah ya maida kowa gida lafiya Wanka itada Babyn aka musu, shitafi bukata a yanzu dan ta gaji sosai Kowa ma baccin sa yai da wuri, Sultan bashida rigima yanada hak'uri baya mata kuka duk jagwalgwalon daya sha na d'auka Abban CHUCHU ya saitu ya dawo hanya, shima 50k da kayan baby haka ya Ka musu, wasu daga cikin yan gidan sunzo ba a nuna musu komai ba tunda duniya ta koya musu Kowa dai yazo lafiya ya koma gida lafiya, kama daga na wasu garin Har na wata k'asar daban anbar Maijego da babyn ta da Hajiya mai wanka lafiya Oga aiki ya tsare shi, sai dai waya, wajan two weeks kenan rabon ta dashi FUTHA tayi kyau tayiwa k'iba mai ban sha'awa Hajiya Mama Maman ta dukkansu k'ok'arin su su gyara yar su. *Remain Last page* @ut@r h@jiy@ [11/10, 8:27 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [10/11 9:39 am] @ut@r h@jiy@✍🏻💅🏻: *FUTUHATUL KHAIR* *®NWA* *©Zainab Y Hussein* *Dedicated to FUTHA LUV* *_THE END, K'ARSHE_* FUTHA tasha gyara, dan wataran Hajiya Idan tabata wani abu kotace tayi tsuguno dashi zata fara kai wallahi nagaji da wannan kayan haka kawai aringa sawa cikin mutum na ciwo da wannan kayan Lallai yarinya ai gatan kenan, Idan ba haka ba wazai kalle ki duk d'okinsa akan ki wallahi saiya dena, Sai maigidan tsalle, karya gado duk zan had'a miki Dariya Mama tai tace wannan drama haka, to ke FUTHA kiyi hak'uri Hajiya gyara take wataran da kanki zaki nemeta ta baki Kai ta sunkuyar tana d'an murmushi, tana wasa da hannun Sultan dayake shan Mamma Wannan Satin FUTHA sukayi arba'in, shima asatin yazo, rud'ewa yai ganin yadda One love tai kyau ta fita sosai tayi fresh sai kace milk ko kazar turawa Ai baiji kunya ba, ko da yake Hajiya tana wajan Mama, laluba matar sa yai, sosai hakan yasashi nishad'i, dan ji yayi kamar sun shekara rabon da jikin su ya had'u waje guda Kallon ta yake yana yaba kyan da tayi ga gashin ta yasha gyara kamar tasan zaizo ga wani sirrin k'amshi da take yi Ga skin nata yai smooth sosai, Babyn ta ya girma Hajiya cewa tai tanada gafin Nono yanda yaron yai girma sosai kamar anyi 3 months Sun zaga dangi na kusa har katsina sunje Maiduguri, koina sunje kowa kuma yai murna Tukwicin Hajiya na gyaramasa mata da tayi kujeran Makka yabata tayi murna duk da tana zuwa amma irin wannan kyauta ta bazata akwai dad'i Kilishi ma ganin tana so haka ta siya mata sosai, tai farin ciki k'annenta dasu sukaje Libiya tunda sun jima basu jeba Fadeela tayi murna, sun zaga dangin Maman ta, har gidan Abokin Abban ta da silarsa Abban ta ya had'u da Maman ta taje yai murna shima Daga nan basu dawo 9ja ba NIGER suka tsaya, lokacin da jirgi ya sauke su tagane wajan Kallon sa tai, kai ya kad'a mata duk jama'ar wajan Bata lura da kowa ba, rungumeshi tai tana hawaye tace Abban Sultan Nagode sosai Allah ya kiyaye mun kai Allah kuma yabaka abinda kake so duniya da lahira Allah yabamu zuri'a ta gari Allah yabamu tsawan rai mai amfani Tana k'irjinsa take wannan addu'a, kanta ya Shafa yace Ameen mata ta gari, komai kike so zan miki Iya aljihuna da k'arfina, kina kiyaye komai nawa nimaizaisa bazan yi abinda ranki zaiyi dad'i ba Hannun Abdallah ya kama yace tawo ga motar ma tazo, abokinsa ya zo ya d'auke shi, gidan Adda Bena taga yayi, nan ma kallonsa tai, of course ina zuwa fa, har Abban Ku ma yazo Gidan suka shiga angyara kamar ba shiba, k'awayenta ta gani ciki harda Ummul fadeela da Hauwa Jabo data taimaki Aunty Meimi lokacin Haihuwa Kuka suka saka antuno da, baran da sukaji tana magana nan wata sabuwar murna aka saki K'awarta Rash tai aure itama tazo wasu kuma basa garin, Lallai mijinta abin alfaharin ta ne, kud'i yaraba musu Abdallah kowa ya ganshi yaga Abban sa, sun jinjinawa kirki irin na FUTHA da sukaji yana hannun ta, Adda tai kukan rashin aminiyar kwarai dalilin ta, ta sauya hali take kula da mijin ta, ta ajiye sana'a gefe takula da gidan ta dole tayi kuka Mak'ota sunzo wasu kuma ta shiga, anmusu abin arzik'i abinci ko ina kawo musu ake Gidan da suka zauna ta shiga tun a soro tasan cewa tafiya tai tafiya, tunda gashi ancanja tsarin komai na gidan Ikon Allah wannan mutumin ta gani ya ganeta itama, wanda tacinyewa abinci a kasuwar duffa dariya yai yace Ashe baki mutu ba, akace kin mutu Abban ki yazo nan yabata labarin yadda akai Matarsa mai kirki, shima kud'i tabashi yai godiya sosai [10/11 10:23 am] @ut@r h@jiy@✍🏻💅🏻: A washe gari suka tarkata suka koma k'asar su ta gado wato NIGERIA🇳🇬, Lagos suka sauka gidan su, shima an k'ara gyara shi yai kyau ancanja abubuwa na gidan sosai Rayuwa wad'an nan ma'auratan sukeshimfid'a wa mai tsafta tafi da ilimin boko dana addini ga Abdallah da sukai masa rik'o na gaskiya da amana yaron kuma ayanzu yak'ara hankali *5 Years ago* Gidan na koma naga meke faruwa bayan dogon lokacin dana d'auka ban waiwayi gidan ba Gidan yana nan yadda nasan shi before, sai gyara da k'awatashi danaga anyi ga wasu flowers da aka k'ara ga kayan wasa daga gefe da lilo dana gani ga paint da aka canja Badan nasan gidan ba, a yankin Ikeja yake, kuma tsarin gidan shine danace bashi neba saboda gyara daya sha Parlour nayi, kai ! Yara nagani wajan su hud'u kuma dukkansu kama suke da Abban su Illa mace kwaya d'aya da tayi kama da FUTHA kusan kansu d'aya yaran macen itace dai k'arama Lallai Allah da iko yake Da fari ya hanaka amma Idan yafara baka, har saika k'osa Kowanne cikin yaran strow ne a hannun su Almara'i suke sha. Babban shekaran sa 5, sai yan biyun kuma 3 sai k'aramar su batafi one year ba Ita tana kan Carpet a zaune fuskanta duk madara ta b'ata tak'i kuma a tab'a fuskar mai aikin gidan da yayunta daga sun daukai tissue zata saka kuka shiyasa suka kyaleta Alamar tafiya naji, FUTUHATUL KHAIR ce tareda mijinta cikin shiga ta alfarma shi kakin sane ajikin sa itakuma Pakistan ne red yamata kyau kamar ajikin ta aka d'inka tana nan yadda take saima kyau data qara yi Daddy kadawo shine baka tashemu ba, munata jiran ka har mukayi bacci Sultan ne yake magana, kansa yashafa yace I'm sorry Boy mun tsaya a border ne, daga airport naso nazarto gida kodan saboda Ku amma bansamu sarari ba Kayi hak'uri kaji, tom Sady, d'aya Bayan d'aya yabi yashafa kansu, twince sunan su Hakeem da Haleem yara kyawawa gashin Maman su suka d'akko Wajan Babyn yayi ya dagata sama yace yarinyar Momi bakiyi missing Dady ba, ko kallon sa bakiyi ba [10/11 11:17 am] @ut@r h@jiy@✍🏻💅🏻: Yana kallon fuskanta da sauri ya mik'awa Momin ta Ita, yace wannan yarinyar sai ke, kalli fuskan ta hala kema haka kikayi kina yarinya? Haba dai saidai kai, nima narasa ina ta koyi haka, badamar ace za'a gyara yanxu kaji kuka kamar zata tsaga gidan Dariya yayi yace, gata da k'iwa kuma koni bata yadda dani, Huum kowa ma haka take masa baran Aheed k'anin ta kenan, tace kaga Idan yazo gidan nan kamar taga dodo Bata yadda dashi shiyasa shima baya kulata, ga wani hali data koya daga tafara shan nono idantacika bakin ta dashi saita bullutso dashi Yan yan yan yan, lallai *ZAHRAN MOMI* kazama ce ke yana magana yana tab'a kuma tun ta dariya tafara masa Kan cinyanta tasakata tafara feeding nata, tafara sha kenan ta tajiyo sallaman Abdallah ai da sauri ta CIKA tafara kiciniyar kwacewa ta sakko wajan sa Shima ganin haka da saurinsa ya tawo, yace *My ZAHRA* oyoyo, wangale baki tafara, Huum kaga wanda kawai batawa k'iwa amma kowa saita gwada masa Farouq ne yayi maganar Dariya Abdallah yasaki yace Abba ina kaga mata nawa miji k'iwa sai dai Idan baso ko Matas?, kamar taji mai yace tasaki dariya Lallai amma ka d'auko mata da k'azanta, eh Abba inaso a haka wataran sai labari.Sai anzo ana layi, badan nace ina so ba da daga kan president governor sai sunzo Dariya Abba yayi yace lallai zanso nayi tsahon rai dan zanga wannan lokaci Abdallah kenan yaro mai hankali da sanin yakamata yanzu haka yanada shekara 15 yayi girma yana SS3 a school FUTHA dai murmushi take tana godewa Allah daya bata miji da dangin miji masu sonta da son komai nata Rayuwa tamata dad'i batada matsala karatunta ta k'are cikin sa'a mijinta na kyautatamata yanamata abinda take so Sai in batace tana so ba Abdallah d'aukan *ZAHRA* yai suka fita, bayan ya goge mata fuska, su kuma yaran d'akin su sukayi Ganin haka shima Farouq yace office yasha ruwa yau, gara aje ayi aikin lada asamawa *ZAHRA* k"anwa ko kani Dariya sosai tayi, haka ta mik'e tana rangaji akayi *MASTER BEDROOM*nima danaga haka k'afafuwana naja a hankali na fice ina kwad'ayin nima Allah yaban Family fin haka ma *Ina Godiya ga Allah mai kowa mai komai daya bani ikon kammala wannan littafi ina rok'on Allah yasa abinda akaji na amfani ayi AIKI dashi, Wanda akasin Hakane a zubar da shi* *Ina Godiya ga writers 'yan uwana da kuke bawa kowa k'arfin gwiwa wajan kanbaba rubutun sa, jini ne ko Na jikin Auta, Auta tana sonku harba adadi* *Aunty Sady Jegal, My STYLICH, Didi Aneesa Nafeesat Anker, Princess Hassy, Zahar Bukar, Queen Meemi Jameela Mohd Ali kuna zuciyar Auta ko da yaushe* *Jabo jabonation Hauwa ta, kina zuciyata Aunty Bilkisu, Faty Axland, STYLICH Anker, Anee Sahaf dukkan Ku kuna raina* *Wanda ban fad'a ba, kuma kuma raina Allah yasani* *Jinjinar ban girma Aunty Mamu, tabarya mai baki biyu* *Yar uwata Rabin raina Yayata Maryam Mohd kina raina, koda yaushe burin ki, ki farantan Nagode miki sosai, Maryam d'in Umma Halima ta ina nan zuwa wajan ki* *@ut@ ce, ta Hajiyan ta Yar albarkar Baban ta* *Ku saurareni cikin wani sabon littafina mai zuwa nan gaba mai taken SO BABBAR CUTA* DOCUMENT MADE BY SALMA SWEET NOVELS GROUP ADMIN. adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *