Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, April 3, 2017

Gangar jikinsa na aura

adsense here GANGARJIKINSA NA AURA 1 Part 1 Posted by ANaM Dorayi on 07:51 PM, 29-Apr-15 Under: Gangarjikinsa ta Aura GANGAR JIKINSA NA AURA JAMILA UMAR TANKO {JUT} ⃣Wata kwarababbiyar mota kirar bus mai kararfatattakekkiyar salansa ce ta tsaya a bakin get dinmakarantar 'yan mata ta gwamnatin tarayya dakegarin Kazaure, wato F.G.G.C. Kazaure. Tana tsayawakondastan motar ya ja kofar ya bude "Barararaa"saboda kwankwatsewar da kofar motar ta yi sakamakon cin ruwa da gafje-gafje da tsabar tsufa.Wani dattijo mai kimanin shekaru saba'in da doriyane ya fito, da wata *yar yarinya tana biye dashiwacce shekarunta basu wuce shekaru goma shadaya ba, Bayan sun furfito kondastan motar yazagaya baya wato but ya dauko wata katuwar akwatin karfe irin ta *yan makarantar wacce akadafka sunan mai akwatin garza-garza da fenti bakiHANNE HABU IMAMU. Ya ajiye gefe ya sake janyowata karamar katifa wacce take daure ya doraakan akwatin, sannan ya dauko wani bokitin karfesabo dal yana sheki shima an fenteshi da sunan mai bokitin wato HANNE HABU IMAMU. Daga karsheya mayar da kofar but din ya rufe ya juyo ya kallidattijon wato Malam Habu ya ce "Baba baka fa cikamana kudin motarmu bafa, gashi har kun sauka"Malam Habu ya sake marairaicewa ya ce "Dana daAllah fa nake hadaka kuyi hakuri kudin da yayi saura a aljihuna ko gida bazai mayar dani ba, sai nanemi ciko kayi hakuri dan Allah, dan haka nemanace ta zauna a maleji yanzu baza ka tausayawatsoho ba, karbi arba'in din?" Kondasta ya sakefusata ya ce "Dalla Baba kana bata mana lokaci gafasinjoji har sun fara tsaki sun kagu suma a kaisu inda zasu. Ka zauna kana mana magiya tun dazumuma fa ba'a bati muke shan man motar da mukejigilar nan bafa, da kasan kudin motar taka bai cikaba me yasa ka hau? Har zaka ce wai yarinyar amaleji ta zauna, maleji ba cikin mota bane? Bakasan har a sittin muke daukar na maleji ba daga inda muka dauko ku zuwa nan nayi maka ragi nace kakawo hamsin dinma gashi kaki biya sai wataarba'in ka bani, kai wallahi Baba saika ciko managomarmu kaji ko? Direban motar dake zaune awajen tuki wanda yake jin duk abinda suke yi, saiyanzu ya waigo inda suke yayi magana ya ce "K.b wai yane? K.b ya ce "Har yanzu wannan tsohon baidaina magiya ba wai shi ayi masa ragin goma kudinyarinyar nan data zauna a maleji, Hamsin nace yabiya, ya wani bani arba'in. Kuma ma dan raininhankali harda cewa kudin aljihunsa bazai mayardashi gida ba, wato yana da kudin, cikawa ne bazai yi ba.din aljihunsa bazai mayar dashi gida ba, watoyana da kudin, cikawa ne bazai yi ba. Malam Habuya danji dadi ganin direban yayi magana ko zaice abar masa amma sai yaji kalamansa sabanintunaninsa gara ma abinda kondastan ya fada masa,cewa yayi in har bazai biya ta dadin rai ba to zasu farka aljihunsa su dauki gomarsu, Malam Habu yarike baki don mamakin irin wannan rashinmutunci, can ya nisa ya ce "Allah Ya kyauta, bari nabaku kudinku abin duk bai kai ga haka ba, yasahannu a alhihunsa na dama ya dauko watacukurkudaddiyar naira biyar ya sake saka hannu a aljihunsa na bangaren hagu ya dauko gudar nairaashirin da kwandaloli guda biyar, ya hadakwandalolin nan guda biyar da cukurkudaddiyarnaira biyar din nan ya mikawa kondosta ya ce"Gashi dana Allah Ya kiyaye. Ba kunya ba tausayintsohon nan yasa hannu ya karbe yana gunani "Daman kana dashi ka tsaya kana bata mana lokaciduk fasinjoji sun kagu, direba ya juyo ya ce "YayaK.b ya baka, sun cika? K.b ya ce "Eh sun cika jamujeJ.J.C. Malam Habu da *yarsa Hanne suka bi motar dakallo har ta hau titi ta kure sannan hankalinsu yadawo kan kayansu. Malam Habu ya kalli *yarsa Hanne wacce hawaye ya gauraye idanuwanta dakumatunta, abin ya bashi mamaki ganin Hanne nakuka alhali kuma ita take son karatu take murna dazasu taho, ya sake juyowa sosai ya kalleta yagahawaye ne ke zubowa daga idanuwanta dayanabin daya, ya ce "*Yar Baba, kukan me kike yi? Karki cemin yanzu bakya son makaranta bayan keaka kira fadar mai gari aka tambayeki kika ce kinaso. Ba'a son raina ba nima na kawo ki makarantarnan ke kika amsa musu. Shine kuma yanzu kikekuka? Idan kinsan bakya so to ni a wajena tafinono fari sai mu juya kafin mu shiga ciki. Kansila da mai gari su suka tilastamin in kawo ki amma badanhaka ba nima bazan rabu dake ba na kawo ki nanuwa duniya, babu wanda kika sani. Hanne tagirgiza kai cikin shesshekar kuka ta ce "Baba bamakarantar bace bana so, rashin kunyar da masumotar can suke yi maka shine ya sani kuka. Malam Habu yaji hawaye ya cika masa ido amma sai yajure yayi murmushin karfin hali ya ce "Allah Sarki*yar Baba, babu komai duniya ce. Duk wanda yagagirman tsohon wani, za'a ga girman nasa. Hakakuma duk wanda ya raina tsohon wani sai an rainanasa, zamani ne ya canja babu sanin girman Allah, ko an hada mutum da Allah kamar an hadashi dasa'ansa, wani cewa zaiyi daina hadani da Allahkarka cuceni Wa'iyazubillah. Ya ci gaba da cewa"goge hawayenki 'yar Baba kizo in dora mikiakwatin mu shiga ciki kada dare yayi min kinga harla'asar tayi. Tasa gefen gyalen da taci damara dashi ta goge idanuwanta kana ta matso ya ciccibiakwatin karfen nan ya dora mata a kai shi kuma yadauki bokiti da katifa a daya hannun sa'annansuka juya suka doshi cikin babbar kofar shigamakarantar, yaci gaba da yi mata nasihohi masuratsa jiki yana nuna mata wannan abin da aka yi masa a gabanta ya zama darasi a wajenta duklalacewar tsoho koma ba tsoho bane na gaba da itakada tayi masa fitsara. Ta zamana ko a ina takekuma kome ta zama ta girmama na gaba da ita.Ta zama mai taimakawa mabukata, kasancewartasan talauci ta kuma dandanashi tana kandandanashi. Masu gadi uku suka iske a bakin kofarshiga cikin makarantar, suna zazzaune, MalamHabu yayi musu sallama gami da mimmika musuhannu, Hanne ma ta duka ta gaishesu, bayan sun amsa, Malam Habu ya ce "Yarinya na kawomakarantar nan, ta ina zanbi mu shiga ciki? Dayadaga cikinsu ya ce "Mikewa zakuyi sosai zaku tararda ofishin Malamai dana shugaban makarantar.Malam Habu yayi godiya suka wuce, har sun danyonisa suka ji masu gadin nan sun kwalla musu kira bayan sun dawo, sai daya daga cikinsu ya kallesusama da kasa ya ce "Dan Allah Malam muna datambaya sai bayan da ku ka wuce tambayar ta fadomana. Malam Habu ya gyara kayan dake hannunsagami da yin murmushi ya ce "To Allah Yasa na sani.Ya ce "Wai shin me kake tambaya ne? *Yar makaranta ka kawo daliba ko kuma mai aiki kakawo gidan Malamai a nuna maka gidan Malamai(staff quaters)? Malam Habu ya ce "A'a daliba nakawo 'yar makaranta ce. Su duka suka kyalkyaleda dariya suna tafawa wani harda buga kafa akasa. Abun ya daurewa Hanne da Mahaifinta kai. Menene abun dariya?Konan ba ita bacemakarantar 'yan mata ta gwamnatin tarayya dakeKazaure? Malam Habu ya tambaya suka ce "Nan cemakarantar daka ambata amma watakila kayibatan kai ko baka ji dai-daiba. Malam Habu ya ce"Batan kai kamar yaya? Daya ya ce "Nan makaranta ce ta 'ya'yan masu hannu da shuni,'yan birnimasu kokari, ba haka kawai dan ance 'yarka tacimakaranta ba kaje ka suyo akwati da katifa kazoka zabi makarantar da ranka yake so ka shiga kacega daliba. Daya ya ce "Ko dai waccan makarantar ceta gwamnatin jiha suka rasa suka shigo nan. Koda yake ko can dinma dakyar su kwashi wannan.Sannan na karshe ya ce "Ku dai ku tsaya babumamaki nan din taci abun ai na Allah ne, Malam inatakardar shaidar taci nan makarantar? Malam Habuya ce "Mu babu wata takardar shaidar cinmakaranta a tare damu, ni dai kansilan garinmu yazo har gida ya ce jarabawar da *yata tayi a birnita fito kuma duk karkararmu ita kadai taci, maigarinmu ma ya turo inje ya shaida min ya ce lallai-lallai nan taci in kawota, ya ce min makarantun'yan mata a Kazaure guda biyu ne data gwamnatintarayya data gwamnatin jiha, ta gwamnatin tarayya taci in kawota. Amma ni babu wanda yayi minzancen takarda. Suka sake kecewa da dariya. Dayaya ce "Malam sai kuyi waje don baza ku shiga bababu takardar shaida, ku koma ku sami kansila komaigarin naku su baku takardar shaida sai kuzo kununa sannan mu barku ku wuce. Yau gashi kusan wata daya ke nan da aka riga aka gamakawo yara har sunyi nisa da fara karatu, kai saiyanzu kake kawo 'yarka. Malam Habu ya ja 'yarsaa sanyaye suka yi waje, zuciyarsu cike damummunar damuwa.Hakika Nigeria muna cikin wani hali lokacin da yake ajiye kayan dake hannunsa a waje,yakamawa 'yarsa akwatin dake kanta suka saukekasa. Suka tsaya suka yi cirko- cirko suna kallon masu gadinnan,wadanda har yanzu basu daina yabo musubakakenmaganganu ba. Malam Habu ya nisa ya ce "AllahSarki rayuwa, Allah Ka fimu sanin halin da muke ciki kaizaka fitardamu, 'yar Baba zauna a gefen akwatinki kinjikafin mugayadda Allah zai yi damu. Isa kansila da maigarisuka ja mana wannan wulakancin. Ni nasan a rina, shi yasa dafarko nakifur da akace za'a kaiki birni daukar jarabawa,kuma kema daakayi kiranki me yasa ki amsa musu? Kika ce kinason karatun, ga irinta nan ai. Hanne ta zauna a hankali jikintayayi sanyi,wanda ko yatsanta wuyar dagawa yake yi mata.Zuciyarta cikeda damuwa, babu abin da take tunawa illakomawarta gida haduwarta da iya Abu kishiyar uwarta da'ya'yanta.Irin tsananin azabar da suke gallaza mata dabautar ta din daake tamkar baiwa alokacin cinikin bayi. Ta ce aranta "Da inamurna zanzo makaranta nabar gidan da banahutawa kuma ban taba hutawa ba sai yanzu. Gashi yanzumakarantar masun koro mu dole mu koma gida. Taci gaba da tunairintataburzar da aka sha da Mahaifinta kafin Iya Abutabar su suka fito daga gida zuwa makarantar nan. Wai itaidan Hanneta tafi babu mai yi mata aikace-aikace su sharawanke- wanke,debo ruwa a rafi ko tuka-tuka. Saboda haka nemataki fur wai baza a kawo Hanne makaranta ba. 'Ya'yantakuma garda-garda maza da mata suna zaune ko tsinke basadaukewa saiHanne wacce bata da uwa a gidan. Allah Sarkihawaye ne ya kecewa Hanne yayi ta zuba daga idanuwanta.Maganar dadaya daga cikin masu gadin keyi ita ta katse tadaga tunanindata dulmiya tana yi. Taji kamar daga sama yanacewa "Kai kauyawa ma da rashin tunani suke dan kawai ance'yarka tacimakaranta sai ka taho ka zabi makarantar data yimaka kawaika sako kai, dubi yarinyar daya kawo sai kace maizuwa tallar kalwa riga a cukurkude, zanin daga kasa ya nadekamar annade tabarma. Takalmin kafarta harda leda tadaure waye zaice daliba ce. Daya ya ce "Danmarar data ci kai kacedandali zata, ta daure kugu tamau. Ina jin ma basu san anadinkakayan makaranta ba (Uniform) balle takalmikambas da safa.Hanne tayi ajiyar zuciya ta hadiye yawun da ya cikamata bakinta tayi shiru, kanta a sunkuye a kasa.Tace a ranta "Lallai ko nafi maye kwakwa dole nahakura damakarantar nan harda kayan makaranta akedinkawa. Wayezai dinka min? Ta sake kallon kayan jikinta tace aranta "Kayan sallar tawa shine suke cewa duk a cukurkude? Niina ganinnayi ado kowa a garinmu da muka zo wucewayana cewaHanne yau kuma ina zaki kika ci ado haka? Su anankazan- kazan suke ganina ashe, dole mu koma gida asheban rabu dawahalar Iya Abu ba. Kuka ya sake kece mata hardashessheka. Malam Habu ya kalleta fuskarsa cike dadamuwa ya ce "Yi shiru 'yar Baba bari zamu san yadda zamuyi mukoma gida. Ni yanzu ke nake ji gashi kudin da yarage mun aaljihuna saura Naira ashirin kacal. Da niyyatainnakai ki makarantar in zan koma gida sai in hau mota daganan zuwatashar Kazaure daga can kuma sai in kama hanyada kafa harBabban- mutum (garinsu) idan dare yayi mun insami waje in kwanta washe gari na tashi naci gaba. Har dai inkarasa kokwana nawa zanyi a hanya. To yanzu ba zai yuwuba tundagaki, sai dai kawai mu shiga mota muje tasharKazauren, ko a bakin tashar sai in siyar da akwatin nan ko katifarkoma dukamu samu muyi kudin motar komawa gida. Hanne tazabura tace "Ka siyar da akwati da katifa fa kace? Kansila aisai yasa a kamaka, cewa yayi fa gwamnati ce ta siya ta bani.MalamHabu yayi kasake yana tunani na wani lokaci maitsawo can yace "To laifin waye? Shi kansila da maigari basu sanda kudi za'a zo makarantar ba, babu wanda ya bamu kosisinsa,kansila kullum yana min alkawarin zai je ya karbokudin da zaayi miki siyayya da kayan makaranta da komai dakomai, har cewa yayi motar gwamnati ce zata zo ta kawoki..Daga karshe ya zo ya fara hanya tun dagagwangwarmarakwatin nan da katifa da bokiti babu abunda yakara kawowa.Bansan wacce shawara suka yi da maigari ba kumadaga karshe suka ce inzo in kawoki haka za'a aiko mikikayayyakindaga baya. To yanzu gashi takardar makarantar cebabu aka yimana korar kare ina ga idan muka shiga ciki aka cemu kawo kudi, muka ce babu ai sai a rakomu da duka. CikinsauriHanne ta ce "Lah Baba na tuna jiya maigari ya aikoda watatakarda da yamma ya ce ta makaranta tace, bakanan. Na karba nasa a akwatina ko itace suke tambaya?Malam Habucike da mamaki da zumudin dauko takardar ya ce"Haba 'yarBaba kina 'yar karamarki kike mantuwa, tun dazufa ake maganar takardar duk baki tuna ba. Yi maza kidaukotakardar in nuna musu ko itace takardar. Hanne tadagaakwatin da sauri ta bude, babu komai a ciki saikayan sawarta kala biyu a cukurkude suke kamar anyi sukuwardoki a kansu.Ta binciko can kasan akwatin ta dauko watadoguwar takardafara ta mikawa Babanta. Malam Habu ya karba dasauri ya doshi wajen masu gadin nan yana cewa "Ga daiwata takarda a cikinakwatinta saiyanzu ta tuna ashe mai gari ya aiko da ita jiya kudai ku duba ku gani ko ita ce. A yatsune daya daga cikinsu yakarba yaduba yana dubawa kuwa yaga takardar shaidar andaukiHanne Habu Imamu a F.G.G.C Kazaure ce wato(Admission letter) Sun sha mamaki kwarai da ganin nanmakarantar kuwataci ba batan kai suka yi ba. Cikin sakin fuska sukayi musuizinin su kwaso kayansu suzo su wuce. Cikinmurna Hanne da Mahaifinta suka kwashi kayansu suka wuce izuwacikinmakaranta. Basu tsaya a ko'ina ba sai a bakin wanibabbangini wanda ya kunshi doguwar baranda da ofishinMalamai.Babu kowa a wajen hatta leburori masu share-share da goge-goge duk basa nan, wajen tsit kamar babubil'adama. Sukasami gindin wata bishiya suka sauke kayansu.Hanne ta hau kan akwatinta ta zauna Malam Habu ya ce "To fawannanshine ko in kula, yanzu kuma ina zamu dosa kokuma wazamu tambaya? Ni wallahi abun nan na makarantarbokon nan ya ishe ni daga nan sai can ana tsattsare ka datambayakamar a lahira mun gama da masu gadi yanzukuma Allah nekadai Ya san wa zamu hadu dashi, kai Allah Yakyauta, wannan shine ake cewa ba shiga ba fita wai anbawamahaukaci gadin kofa. Shigowar wata dalleliyarmota ce Jeeplaunin koriya (dark green) wacce ta tunkaro indasuke, ita ta katsewa Malam Habu surutun da yake yi. Ta zo dafda su tatsaya babu abinda yake tashi a cikinta sai sautinkida dasanyin A.C maza ne samari guda biyu suka fitodaga gani wa ne da kaninsa, kanin yana sanye da kayan bautarkasa ajikinsa wato (N.Y.S.C) Yayan kuwa wata tsadaddiyarshadda cefara sol a jikinsa sai kamshin wani tsadadden turarene yake tashi. Abunka da kauyawa sai kallo suke dukkauba da *yar,kanin ya bude but din baya ya dauko wata Jakarkaya, yamayar ya rufe ya ce da wansa "Yaya Habib, na godesai dai nace maka Allah Ya kiyaye hanya. Yaya Habib yayimurmushiya ce "To madalla. Allah Ya bada sa'a sai yaushekuma zaka zomana weekend? Ina fatan dai wannan karan zakayi kamar wata baka zo ba ko?Su duka biyun suka tuntsire da dariya, kanin yace "Ai Yayaranar juma'ar nan zaka ganni a gida ko ba'azodaukana ba mazanzo Kano, haba ai sai jini na ya hau zama a kauyein ba dole ba wa zai iya? Yayan yana dariya ya mikawakanin hannusuka gaisa ya ce "To Allah Ya taimaka, ina ganinranar juma'arda zaka zo may be baza mu hadu ba saboda dasassafe zan tashi zuwa america kai kuma nasan sai da yammazaka tahosai an tashi *yan makaranta ko? Kanin ya ce "Ehkuwa bazamu hadu ba Allah Ya kiyaye hanya Ya dawomana da kai lafiya, Yaya akwatinan auren da nawa da naka yazamo iridaya. Yaya Habib ya ce "Insha Allahu, Yaya Habibya shigamota har zai ja kofar motar ya rufe sai ya juyo yakalli Hanne da Babanta ya ce "Salamu alaikum" Malam Habu yaamsagami da daga hannu, Yaya Habib yaja motarsa yajuya ya nufikofar fita kanin na tsaye yana daga masa hannu.ayan da motar Yaya Habib ta kure, idanuwansuduka na kantasannan hankalin kowa ya dawo jikinsa. TunaninHanne yakoma ga kallon kyakkyawan ginin makarantarginin bulo da bulo,yaune rana ta farko da take tunanin take saran zatakwanta a dakin ginin bulo ba gidan kasa ba rufinazara. Ta cea ranta "Cafdijan yau kuwa zan iya bacci? Anyabazan ringa jin sanyi ba a wannan dogayen gininnikan. Bata sansanda tayimurmushi ba har hakoranta suka fito, sai tawayence ta kifakanta akan cinyarta kada Babanta ya ganemurmushin dadi take. Kyakkyawan saurayin nan ya tunkaro indasuke yanarataye da jakarsa a kafadarsa, ya yiwa Malam Habusallamagami da dan dukawa kadan, kana ya wuce su yajegindin wata bishiyar dake kusa da tasu ya daga wani benci yazauna yaajiye jakar kayansa a kusa dashi yaci gaba dakallon Hanne daMahaifinta. Can Malam Habu yaje ya same shi a indayake zaune ya ce "Dan Allah *yan samari kai maka'aikacine ananko kaima bako ne? Yayi murmushi ya ce "Yaya akayi Baba?Malam Habu ya ce "Yarinya na kawo makaranta tundazu banga kowa ba balle in tambayeshi hannun wa yakamata indankata? Saurayin nan ya gyara zama gami da cirehular dakekansa ya ce "Daliba, daliba ce wannan? Malam Habuya ce "Eh nan aka ce na kawota kuma gama takardar canbari ta mikogama korarmu akayi dazu da babu takardar, yakwalla kira yace "Hanne kawo takardar nan ta dazu.Cikin sauri Hanne tasa hannu a cikin bokiti dakegabanta tadauko takarda tazo ta mikawa Babanta da hannubiyu ta dukahar kasa. Babu abinda wannan saurayi yake saikallon Hanne sama da kasa kayan jikinta yake kallo da takalmindakekafarta wanda ta daure da leda saboda ya tsinkekudin naninma aiki ne, wata uwar danmara kai kace dambentsiya za'a kwasa, wuyan, hannu da kafa tsakiyoyi. Saurayinnan ya kulada lallai Hanne ita kanta tana jin kunyar shigar nantata ganinkallon da yake yi mata, sai yayi sauri ya fara dubatakardar da Malam Habu ya mika masa. Ya karance tsaf, sannanya dagoya ce "Hanne Habu Imamu ko? Tace "Eh, ya ce "ToBaba saikun dan jira don nima nan Malamin nake jira gashitakamaimai ma ni bansani ba ko yana makarantar kobayanan don nima shigowata kenan. Malam HabuyayiHamma gami da yin dan siririn tsaki ya ce "Yaroyanzu bayadda za'ayi ka karbi yarinyar nan, dole sai waccan din ya zo? Saurayin ya ce "Ni Malami ne amma kuma bapermanentteacher ba bautar kasa (service) nazo yi, a ka'idarwannanmakarantar kuma senior master ne ya kamata ya karbetamusamman ma kasancewarta sabuwar daliba ce.Gashi yau lahadi, dama litinin ce ko sauranranakun aiki lokacin principal tana nan, da sauranpamanent teachers duk sai su karbeta koda seniormaster baya nan, amma yanzu ku jira kadan idannan da minti talatin bai dawo ba, zan tashi nima nashiga staff quaters din na gani ko yana ma cikin makarantar dan nima shi nake so na gani zan karbimukullan gidana. Malam Habu ya ce "To Allah Yakawoshi lafiya bari nayi sallar la'asar, nasan biyartayi ko sallar la'asar bamu yi ba. Yaro ina buta? Yanuna masa wani fanfo can kusa dashi kuma dazagayeyyen waje nan ne Masallaci. Malam Habu ya ce "To madalla. Ya kalli Hanne wacce ke tsaye agefe har yanzu ya ce "*Yar Baba koma kanakwatinki ki zauna zanje nayi sallah kinji. Cikinsanyin murya ta ce "To, ta juya ta doshi wajenakwatin. Malam Habu ya bita da kallo zuciyarta cikeda tausayinta ganin yininsu guda babu abun da suka ci tun dan kokon safe da suka dan kukkurbaa tsattsaye bala'in Iya Abu ya hanasu su zauna susha sosai. Malam Habu ya girgiza kai alamartausayawa kansu da kansu ya ce "Allah Sarki *yarBaba hakuri dai za ki yi, ki kuma ci gaba dayi.Sannan ya juya ya nufi wajen fanfo. Kyakkyawan saurayin nan na zaune yana kallonsu zuciyarsacike da alamomin tambaya da tsananin tausayi. Canya nisa yayi ajiyar zuciya ya zaro gilashin dakealjihunsa ya saka a idonsa gami da cusa hular dakehannunsa a cikin aljihunsa na wando yasahannunsa ya dafe habarsa yaci gaba da kallon Hanne dake zaune kan akwatinta tayi lamo tanatunani ba tare da tasan wani na nan gefenta ta cikingilas yana kallonta ba. Ya ce a ransa "Wadannandaga wanne kauye suke?Sun kuwa karanta takardar dake hannunsusunsan me ya kamata su tanada suzo dashi? Kaibasu san dokar da aka rubuta ba a jikin joininginstruction din nan ba. Lallai kuwa da sun san meaka rubuta da baza taci uwar danmarar nan ba tashigo makarantar nan haka ba. Bayan kamar tafiyar Malam Habu da minti ashirin sai gashi yadawo. Ya zo ya wuce ta gaban saurayin ya ce"Sannun ka da hutawa, ya katse tunanin da yakeya ce "Yauwa Baba. Malam Habu ya kara da cewa"Har yanzu dai kaga shiru baizo ba ga rana nan nashirin faduwa yau kuwa anya mai karbar yaran nan zai dawo? Yayi murmushi ya ce "Ina ganin kakawo duk abubuwan da aka ce ta siya da kudinmakaranta zan yi kasada na karbeta yanzu in yasoranar litinin wato gobe idan mutum yazo ya rubutarisitai yanzu sai nayi magana da masu gadin get dinHostel su kirawo prefect din.... Malam Habu ya matso kusa dashi ya ce "Yaro fadamin da Hausasosai na gane me kake cewa? Har da wani abu dazan kawo nan gaba? Ya ce "Eh Baba, ai a rubuce ajikin takardar aka rubuta za'a dinka mata kayanmakaranta har kala hudu, wanda zata sa idan zasuaji da wanda zata saka a dakunansu, dana wasanni (sport) duk an rubuta kuma lallai-lallai sai da kayanmakaranta za'a karbeta ba zata ta saka kayan gidaba, sannan daga karshe aka rubuta zata zo dakudin makaranta (school fees) shi kuma dakesabuwar zuwace sai kun biya sama da dubu.....Malam Habu ya katse shi da sauri ya ce "Tsaya yaro karma ka kirawomin wadannan dubunnai. Ta faruta kare wai anyiwa mai dami daya sata, yaro nagode madallah, sai anjima. Malam Habu ya juya batare da ya jira amsa daga bakin saurayin nan ba yadoshi inda Hanne ke zaune da saurinsa kamar zaikifa cikin gaggawa, ya ce "*Yar Baba tashi maza mu tafi ga magariba ta kawo kai. Cikin sauri ta mike yaciccibi akwati ya dora mata akai ya sungumi bokitida katifa suka kama hanyar get din fita. Sunyi takudaya biyu sai sai suka ji magana kamar daga samaance "A'a Baba ina zaku kuma? Su duka suka juyadan ganin mai maganar sai suka ga wannan kyakkyawan saurayin ne ya taso yazo wajensu.Malam Habu ya ce "To yaro me zamu yi in ba tafiyaba, dubunnan kudi fa naji kana kira, kuma ka tsayacak ka kalleni dani da dubu daya ma waye ya ajiyewani? Daman kansilan garinmu ne da maigari sukasani dole na kawo *yar nan makaranta, suka ce za'a aiko da kudin, na tabbata har ga Allah basusan kudin yakai dubunnai ba da suma basu tankaba. Kuma kudin gwamnati ba'a bashi babu yaddaza'ayi nazo na ajiye yarinya a makaranta babukudin makaranta babu kayan makaranta na ce abimu bashi zamu kawo ba. "Wannan ba zai yiwuba, inji saurayin. Malam Habu ya ce "To ka gani cewasuka yi na zo na kawo ta za'a aiko da kudin kumayadda naji kalamansa shi kansilan a tunaninsakudin makarantar bai wuce dari uku ba, bai sandubunnai bane kuma koda shine yazo ya kawotaaka kira dubunnan nan cewa zaiyi ta fasa karatun. Don karamar hukuma baza ta biya wadannanmakudan kudin ba.Saurayin nan yayi murmushi ya girgiza kaiya ce "Amma Baba bai kamata daga kirandubunnan nan ka kwasheta haka da sauri kacezaku tafi ba. Malam Habu ya fara jin haushinsaurayin nan, ya ce a ransa "Wai shin wannan dukzancen nan da ake bai gane ba ne? Makaranta sai da kudi kuma babu kudin jiran me zanyi, ko shi baisan babu ba ne? Saurayin nan yaci gaba da cewa"Baba kuzo ku ajiye kayan nan bai kamata ka juyada yarinyar nan ba, ai bai kamata ba. Ta cimakaranta har kun shigo cikin makarantar sannanku kwasa ku tafi ka ce ka fasa, babu fa abin da Uba zai yiwa *yarsa a duniya in ba ya bata ilimi ba,yarinya kamar wannan ai kamata yayi tanamakaranta tunda bata isa aure ba, me zata yi agidan? Malam Habu ya sake jin haushin saurayinnan kamar ya doke bakin da yake masa wadannankalamai ya ajiye bokiti dake hannunsa ya ce "Yaro, wai shin a harshen Hausa idan akace babu me akenufi? Yayi murmushi ya ce "Baba kenan, na gameduk dalilan da kake nuna min yanzu, ni kuma abinda nake so na rokeka shine ka fasa tafiya da itatunda ka kawota har cikin makarantar ka kyaletatayi karatu. Abun da ya kamata ka tambayeni shine tayaya zata yi karatu tunda babu kayan makarantababu kudin makaranta? Malam Habu ya ce "toyanzu nasan ka gane babu,ta yaya zata yi karatubabu kudin makaranta babu kayan makaranta?Kyakkyawan saurayin nan ya ce "Yauwa Baba kayitambaya mai kyau, amsar tambayar ita ce in Allah Yaso Ya yarda Hanne zata yi karatu in har kaamince ka yarda zaka ringa turo ta makaranta dazarar hutu ya kare ba sai ta fara ba kace baza tadawo ba ka cire ta.Idan kayimin alkawarin haka kuzo ku ajiyekayan nan ka tafi ka barta. Malam Habu yayi jigumyana tunani, a ransa ya ce "Wannan yaron me yakenufi? Hanya zaiyi mana a dauki Hanne babu kudinmakaranta babu kayan makaranta ko kuma yayaza'ayi? Bana tunanin dai shi zai biya mata kudin makaranta harda dubunnan da ko karamarhukumar mu baza ta iya biya mata ba yaddazamanin nan ya canja masu kudi basa taimako,babu yadda za'ayi yaron nan ya zare makudankudi ya baiwa yarinyar da bai santa ba bai tabaganin ta ba bazan bar *yar Baba a makarantar nan ba in tafi ta wulakanta ba, wacce bata san hanyarda zata bi ta koma gida ba idan an korota. Yanzuakan Naira goma masu mota suke kokarin sudanneni su dauka ina ga dubunnan kudade gakayan makaranta har kala hudu waye zai dinkomata? Saurayin nan ya katse Malam Habu daga tunanin da yake yi ya ce "Baba tunanin me kake yine? Karka yi kokonto ba zaka yi dana sanin barinHanne a makarantar nan ba in Allah Ya yarda babuabin da zai sami Hanne sai alheri da kwanciyarhankali ka tsarkake zuciyarka ka danka Hanne gaAllah wanda a koda yaushe Yana kallon halin da bayinsa suke ciki na kunci kona farin ciki, sannanka danka Hanne amana ce a wajena. Ni kuma namaka alkawarin zan karbi amana na rike. Cikinsanyin zuciya da gamsuwa da kalaman saurayinnan Malam Habu ya juya ya kalle shi ya ce "AllahSarki duniya wani ya munana maka wani kuma ya dadada maka. Yaro tunda ka ce Allah na yadda kakuma ambaci amana, amana kalmace mai girmamai wuyar rikewa kace zaka rike tsakaninka daAllah, na gode yaro, Allah Yayi maka albarka Yabiya maka bukatunka. Abin da kayi min UbangijiAllah Yayi maka fiye da haka, *yar Baba muje mu ajiye kayan. Suka juya harda saurayin wajen bencinda yake, Malam Habu ya kama akwatin dake kanHanne ya sauke mata ya juyo ya kalli saurayin nandake zaune akan benci ya ce "Yaro bazan gaji da yimaka godiya ba.Madalla Allah Ya yi maka albarka zan tafi nabarku lafiya, af kaga ko sunanka ban tambaya ba.Saurayin nan yayi murmushi ya ce "Sunana Haisam,Baba. Malam Habu ya ce "To madalla. Ya juya yakalli Hanne wacce ke tsaye idonta ya ciko da kwallaya ce "*Yar Baba zan tafi na barki ga Allah na barki ga wannan bawan Allah. Sai ta rushe da kuka takoma kan akwatinta ta zauna ta kifa kai a gwiwatana kuka. Hawaye ya kecewa Malam Habu ya ce"Nima ba'a san raina zan tafi na barki ba Allah Yakaddara saduwarmu. Ya juya ya kalli Haisam ya ce"Yaro mai wuyar suna har na manta sunan(fatan Yayarmu ma Zee zata iya rike sunan, kodayake ita 'yar birnice, loz) na tafi, sai wata rana. Haisam ya ce "To Baba Allah Yakiyaye. Malam Habu ya juya ya fara tafiya yana facemajina yana goge hawaye da gefen babbar rigarsa,sai yaji muryar Hanne ta ce "Baba ya juyo ya ce"*Yar Baba. Ta taso da gudu ta karaso inda yake takama gefen zaninta ta kwance sai ta dauko wasu cukurkudaddun *yan Naira ashirin guda hudu tace "Baba karka tafi da kafa gashi ka hau mota.Haisam dake zaune har yanzu akan benci yanakallonsu sai da yaji kwalla ta cika masa ido dontausayin Uba da *yarsa. Malam Habu ya ce "AllahuAkbar, *yar Baba Allah Yayi miki albarka. Allah Ya baki ilimi mai amfani, kinji? Waye ya baki harmurtala hudu? Hanne ta ce "Dana shiga makwabtanayi musu sallama suka babbani wasu, saurankuma kudina ne da nake tarawa tun na yawonsalla. Malam Habu ya ce "Kya bani duka ingomurtala biyu ni na dauki murtala biyu, kema ki rika siyan *yar gyada kya zauna haka kina ganin yarasuna siye-siye ke bakya siyan komai? Hanne ta ce"A'a Baba murtala biyu baza ta kai ka gida ba, banaso ka shiga mota kudinka bai cika ba, kana rokonayi maka ragi irin na dazu. Malam Habu ya sakekecewa da kuka ya ce "To *yar Baba na gode na tafi na barki ga Allah baki da kowa, baki da komai,ba ki san kowa ba, Ya juya ya tafi. Hanne na tsayehawaye yana zuba daga idanuwanta tana kallonMahaifinta yana tafiya yana waiwayenta.Taji wani kululun bakin ciki marar misali akirjinta da mummunan tashin hankalin rabuwa daMahaifinta, yaune ranar da ta taba rabuwa daMahaifinta daidai da rana daya basu taba rabuwaba. Gashi a yau ya kawota inda bata san kowa baya juya ya tafi ya barta. Hawaye ne mai radadi yake zubo mata har sai da ta daina hango fararenkayansa ya kure, sannan ta yi ajiyar zuciya tasagefen mayafinta ta goge idanuwanta ta juya tadawo kan akwatinta ta zauna. Haisam na zauneakan benci yana kallonsu zuciyarsa cike datsananin tausayi ji yake wani abu yana yawo a cikin kansa, saboda wani abu guda daya daya bashimamaki ya bashi al'ajabi, shine ganin yadda Hannetake da Mahaifinta suna cikin tsananin talauci ammasuna da wadatar zuci. Haisam yaci gaba da kallonHanne wacce take zaune akan akwati a gabansa tasunkuyar da kanta kasa tayi shiru kamar mai tunani, amma hawaye na digowa daga ganintahankalinta a tashe yake tana cikin damuwa. Yagyara zama gami da zare farin gilashin da yakefuskarsa. Ya ce "Hanne, kukan mai kike yi ne?Bakya so ki zauna a makaranta kiyi karatu kamarsauran yara, kin fi so ki koma gida ki zauna da Baba? Hanne ta girgiza kai alamar a'a, ya ce "Tomeye kike kuka? In kinsan bakya son makarantarnan yanzu nayi sauri na tsayar da Babanki kafinyayi nisa sai ku koma gida. Hanne tayi sauri ta ce"A'a bana so na koma gida, ya ce "To ai kuka kikemeyasa kike kukan tunda kina son makarantar? Bakya son ki koma gida inda zaki yi wasa kuyiwake-wake da kawayenki a dandali? Hanne tayidan murmushi ta sunkuyar da kai. Haisam ya cigaba da cewa "Ni kuwa na dauka danmarar nan dakika ci ta zuwa wake dandali ce. Hanne tayi narai-narai da ido kamar zata yi kuka ta ce "Ni ba'a barina naje dandali wasa. Kullum aiki nake yi sai daiinzo in wuce su in zani debo ruwa. Haisam ya sakegyara zama ya ce "Ban gane ba sai dai ki zo ki wucesu in zaki debo ruwa? Ke kullum a debo ruwa kikebakya zuwa wasa? Hanne ta ce "Eh, sai dai suSaude Yayyena da kanne na ne suke fita wasa.Haisam ya ce "Ina Mahaifiyarki take? Hanne tasake saka gefen gyalenta ta share hawaye ta ce"Tun ina shekara biyu ta rasu. Yaji gabansa yayanke ya fadi ras, saboda yanzu ya gane Hanne agidansu tana cikin halin wahala kasancewarMahaifiyarta ta rasu da alama kishiyar Uwa tana wahalar da ita. Allah Sarki Hanne ya fada a ransayayin daya kura mata ido. Hanne ta bashi tausayida, a yanzu kuma ta sake kara bashi tausayi akantausayi wanda badan ya daure ba da zai iyarushewa da kuka. Can bayan sun dauki wani lokacimai dan tsawo babu wanda ya sake cewa komai. Dukkaninsu kansu a sunkuye a kasa suna tunani,Haisam ya rike kai da hannuwansa guda biyu canya dago ya kalli Hanne ya ce "Yanzu dai a gidankuke kadai Babarki ta haifa kenan baki da Yayye ko?Hanne ta ce "Eh. Ya ce "Shine kuma ake saki deboruwa kullum. Hanne ta ce "Ba debo ruwa kawai ba kullum ni nake wanke-wanke, shara, wankinsu, dakai dabbobi kiwo daga can nayo musu ciyawa.Haisam ya buga kafa a kasa ya ce "Kai wannanwanne rashin imani ne haka? To ya akai kike zuwamakaranta? Hanne ta ce "Sai wajen sha dayan ranakoma wataran bana zuwa, tun ana min dukan makaranta har suka daina su Malamai. Shine waniMalami ya je ya sami mai gari ya ce a yiwa Babanamagana a dinga turoni makaranta da wuri tundaina da kokari, Haisam ya ce "Sai da maigari ya kiraBabanki ya fada masa sannan ake turakimakarantar da wuri? Hanne ta ce "Cafdijan shima Baban ya isa? Ya ce "Kamar yaya bai isa ba.Ta ce "Shima tsoron Iya Abu yake, matar tasazaginsa take,*ya*yanta suyi masa, sai dai in ana dukana inakuka shima yadinga yi. Hawaye ya sake kece mata, shima ya jikwalla ta cika masa ido, ya dauko wani hankici fari kal a aljihunsaya gogeidanunsa ya mika mata, ya ce "Yi shiru Hanne dainakukagoge hawayenki. Ta karba ta goge. Haisam ya ce"Bari na danyi miki tambayoyi naji kina kokari? What is yourname?Hanne ta ce "My name is Hanne Habu,Ya ce "Howold areyou? Ta ce "I'm eleben years old. Wich school areyou? Ta ce "I'm in Babban-mutum special primary school.Haisam yayidariya ya ce "Hanne Habu haka kike da kokari? Toke da bakyazuwa makarantar sosai ya aka yi kika koyi dukwannan? Hanne tayi murmushi ta ce "Ai daga baya maigariyasa akakirawo ita iya Abu da kanta taje fada ya sakashaidu ya ce"Duk ranar data hanani zuwa makaranta ko namakara sai ya kaita kara local goverment. Sannan take barina natafimakaranta da wuri sai dai idan na dawo tayi tadukana tanacewa ga wanke-wankenta nan harya bushe natsaya a hanya ina wasa. Haisam yayi tsaki ya girgiza kai alamartausayawa.Yayi gyaran murya ya ce "Hanne ina so kiyi minalkawarin zakidage kiyi karatu duk rintsi duk wuya. Kar ki zo kifara ayi hutu ki koma gida kiga kawayenki da yayyanki sunagida basa zuwamakaranta kema kiki dawowa. Hanne ta ce"Kwarankwatsazan dawo.(hahah. Inkikayimata dariya bazancigabarmikiba,'Eh' dake nake Zee ) Haisam ya kece da dariya (subhanallahi, tinda shima yayi to kema danyi amma kadan),ya ce"Kwarankwatsabarantsuwa bace wallahi Allah za ki ce. Hanne tayidariya ta ce"Mantawa nayi Malamin makarantar Islamiyya yahana mu cewa kwarankwatsa. Haisam ya ce "Kina zuwaIslamiyyakenan? Ta ce "Eh, ada makarantar allo muke zuwadaga bayaaka bude makarantar Islamiyya da yamma dakuma dare duka ina zuwa. Haisam ya ce dakyau Hanne yanzuidan anyihutu kin koma gida sai kici gaba da zuwa taIslamiyya karkifasa zuwafa kinji? Hanne ta ce "To. Haisam ya cigaba da kallonta har sai da Hanne ta fara jin kunyar kallonda yakemata sannan yayi murmushi ya ce "Hanne dukwannankwalliya ce kika yi a fuskarki, ta zuwa makarantace? Hanne tayi murmushi ta sunkuyar da kai kasa tana rurrufefuska dahannu ta ce "A'a ba kwalliya bace. Ya ce "Gashi nankinrambada kwalli kinja wata doguwar jagira kinyifashin goshi da kwalli kinyi digo-digo duk fuskarki kice bakwalliya bace. Gawannan tsakiyoyi da kika jifga a wuya da hannuhar kafarkima kin daura, Yana dubanta yana dariya. Hannan tace "Eh sarkar salla tace Baba ya siya mun. Ya ce "Kingananmakarantar an hana sawa idan Malamai suka ganizasu kwacesu tsittsinka miki, ciro su ki bani in ajiye miki saianyi hutu in zaki tafi gida na baki. Cikin sauri taji zancentsittsinkawa taciro ta bashi, yadda take bala'in kaunar sarkokinnan natabata son abun da zaisa ta rasa su. Haisam ya karbayana jujjuyasu yaga wasu irin tsohon wuri ne aka jera sucikin liloaka daura ya ce a ransa "*Yan kauye suna gayu.Yayi murmushi ya jawo jakar kayansa ya budewanikaramin zip ya zuba ya mayar ya rufe. Ya juya yakalli Hanneya ce "Kuma a cikin akwatin naki bude in gani kokinzo da wani abunda dokar makaranta ta hana. Hanne tatashi dagakan akwatin ta bude ya karkato ya leka akwatinbabu abundaya hango sai tsummokarai, cikin sauri ya ce "Hanneme wancan nake hangowa kamar miciji a cikinakwatinki? Hannetasa hannu ta zaro wani dan siririn gyale baki yakanannadeya kudindine ta ce "Gyale ne ba miciji bane. Haisamya kyalkyale da dariya ya ce "Na dauka kofi kika yiminna miciji.Hanne ma tayi dariya ta ce "Gyale na ne dan bansaruwa bana kadeshi shiyasa ya cukuykuye, ya sake lekaakwatin sai ya hango wani dan dogon karfe mai huda huda ajikinsa, jikinsakamar farar azurfa yana kyalli ya ce "Hannewannan fa, karfenmenene? Dauko muga. Hanne ta yi murmushi tadauko karfen ta mika masa ya karba ya jujjuya bai san ko meyeba ya ce"Wannan kuma na maye. Hanne ta ce "Idan najekiwo nakeyiwa dabbobi busa dashi, abun busa ne. Haisam yace abun busa kuma? Hanne ta ce "Eh kawo ka gani. Ta karbikarfen tamayar da akwatin ta rufe ta koma kan akwatinta tazauna takaikaice ta fara busawa Haisam wannan karfen kaikace Sarkin busar Sarki ne yake yi, karin busar mai dadi daalama daiwaka ce, Haisam ya buda kunnuwa yana sauraroya baza idoyana kallon yadda take yi.Can ta kyalkyale da dariya ta ce "Haka nake yi.Haisam yayimurmushi ya gyara zama ya ce "To ni abunda bangane ba,kamar yaya sai kinje kiwo kike yi? Daman a wajenkiwo ake yin busa? Waye ya koya miki kuma? Nan da nanHanne tacanja daga yanayin farin cikin da fara'a da sakinjikin da takejikinta yayi sanyi ranta ya baci. Haisam ya ce "Yakika canja nan da nan daga tambayarki? Hanne ta rushe dakuka ta kifakai da gwiwa, Haisam yayi matukar mamaki daganin wannanhali da Hanne ta fada yanzu- yanzun nan ya ce"Yaya kina dariya ki koma kuka, Hanne dago kanki. Ta dagoya ce "Gogehawayenki. Ta goge. Ya ce "Fada min meye nakukan? Hanneta ce "Wani abu na tuna shine ya sani kuka. Haisamya ce "Meye abun da kika tuna? Hanne ta sa hannu tasake gogehawayen da ke idonta ta dauko abun busar dakekan cinyartata rike a hannunta tana jujjuya shi.Tace kullum dasafe nake fita kiwo da raguna da akuyoyin iya abucan dawa. Bana dawowa sai da yamma musammanrabar asabar da lahadi. To awajan kiwo ne nakehaduwa da wani tsoho mai suna malam saleh. Wani lokaci sai yazo ya wuce ni ina kuka idan yunwa tadameni don yini nake anan kuma ba.a kawominabinci. Har dai rannan ya zo ya sameni a gingininuwa ina kuka. Yayi ta tambayata dakyar dai nagaya masa yunwa nake ji. yace '' ba.a kawo minabinci daga gida ?nace ba.a kawomun kuma bana zuwa dashi. Ya ce '' ina babata? Nace ta rasu'' shineya ce min kullum zai rinka bani abinci ina ci dakekullum da rana daga gidansa ake kawo masaabinci nan wajen kiwon rigarsu tana nan kusakusa da garinmu , shine kullum muke haduwadashi yana waka harya koyamin nima nakoya. Sai ya ce ya barmin abun busar tunda na iya, ko bayanransa dansa zai ringa kawo shanunsa datumakinsa kiwo na dinga yi musu busa. Bayan nannaga kwana biyu naya zuwa kiwo bana ganinshanunsa kuma. Hankalina ya tashi naji duk banajin dadin kiwon ni kadai babu wanda muke zama muyi hira muyi busa muyi waka tare. Sai da akadade naga shanunsa da tumakansa an kawosuwajen kiwo amma ba malam saleh bane wanisaurayi ne. Naji gabana yana ta faduwa ko lafiyaina malam saleh yake? Naje na tambayi yaron sai yace shi dansa ne kuma babansa malam saleh satinsa biyu da rasuwa shine a duk sanda naje kiwo nagadabbobinsa sai suyi ta bani tausayi ina kuka''hanne ta goge hawayen da yake zubo mata haisamyayi ajiyar zuciya. Zuciyarsa cike da tausayin hanneya ce a ransa'' hanne yarinya karama tasan bacinrai, tasan tashin hankali ta rasa kowa da zai tarairayeta wanda zata gani taji dadi baya gamahaifinta. Allah sarki , na yiwa allah alkawaribazan kyale yarinyarnan taci gaba d tagaiyara ba''ya juyo ya kalli hanne wacce har yanzu take rike daabun busarta a hannunta tana jujjuyawa.Yacekawo abun busar shima na ajiye miki, idan ba haka shima malamai zasu kwace'' hanne tayi murmushita mika masa ya karba ya jujjuya ya bude zip dinjakarsa inda ya saka tsakiyoyin nan nata ya saka yamayar da zip din ya zuge ya ce'' yanzu abunda za.ayi kije kicin gashi can ya nuna mata da hannunsaya ce kice uwar biyu, tazo inji malam haisam kinji ku taho tare'' hanne ta mike cikin ladabi tana maiamsawa cikin ladabi ta nufi inda ya nuna mata tanatafe tana kara tsuke damarar data ci da gyale akugunta.Haisam ya bita da kallo har ta kure yayimurmushi ya girgiza kai'' bayan tafiyarta da kamarminti biyar sai ga hanne da uwar biyu sun taho tare bayan uwar biyu ta gaishe da haisam durkuso harkasa duk da ta haifeshi tama yi jika dashi amma aidurkusama wada ba gajiyawa bace irin abunalherin da haisam yake yi musu ita da abokanaikinta na kicin sune masu dafawa yan makarantaabinci. Duk ranar da yake duty idan yazo kicin duk sai ya bisu da kudi dukkaninsu don haka allahallah suke malam haisam yazo kicin bayan sungaisa ya ce'' uwar biyu wata alfarma nake si kiyimin idan baza ki takura ba '' uwar biyu ta sakegyara gwiwoyinta da ta durkusa tace'' haba malamhaisam menene ni kuwa a duniya zaka nema ina dashi na takura ai babu sai dai ma nayi murna yauharka nemi wani abu a wajena , mai yi maka kansada kafarsa. Kana yi mana alheri allah ne zai sakamaka da alherinsa'' haisam yace '' amin na gode .Ba wani abu bane daman wannan yarinyar da kikagani kanwatace amma daga kauyenmu taci makarantar nan babanta ya kawota dazu. Tokasancewar acan basu iya karatuba basu san ancea diko kayan makaranta ba da sauran saye saye .To shine naga dasu koma gida gashi garinbakusaba shine nace zan baki ita ki tafi da itagidanki kamar kwana biyu haka kafin na diko mata kayan makaranta( uniform) da sauransiyayya sai tazo ta koma hostel. Uwar biyu tace''allah sarki malam haisam ai wannan ba wani aikibane babu komai ai sai mu tafi daman na gamadaure ledata tafiya kawai zamu yi'' haisam ya ce'' tona gode '' yasa hannu a aljihu ya dauko kudi ba tare daya kirda ba ya mikawa uwar biyu yace '' toga wannan don ku samu ku saisayi dan abundababu'' uwar biyu ta karba zuciyarta cike da farinciki da mamaki irin wannan yawan kudin da koalbashinta na wata baikai wannan haka ba, gashidaman wata yayi nisa. Tayi ta godiya da da shi albarka har ya gaji da amsawa. Ya kalli hanne yace'' hanne inaga yau duk a wunin nan baki ci abinciba ko? Hanne ta sunkuyar da kai tayi murmushitace'' na karya da safe'' uwar biyu tayi caraf tacea.a.a tin karin kumallon safe kuna ta tafiya ko?Haisam yace nisa , don haka uwar niyu kuje ki bata abinci taci ta koshi.Haisam yace ki siya mata tsiren nan na bakintasha dan alla '' uwar biyu tace to in allah ya yardayanzu kuwa'' haisam yaci gaba da cewa'' sannan kisai sabulun wanka da mai me kamshi ki bata tayiwanka , karki barta ta sharba yanxu duk fuskartata kwabe da kwalli. Hanne ki daina yin wannan dige digen kinji ? Hanne tace to uwar biyu tayidariya tace'' ai da haka suma zasu zamo 'yan matasu koyi yadda ake kwalliya me kyau irin na yanboko ko hanne? Haisam yace'' ina ganin har kantasai an wanke , anyi mata sabon kitso, ko kinyi kitsomuga kan? Hanne ta zame dankwalinta ta durkuso da kanta ta nuna musu wayyo allah kowa ya kallikan hanne zai san bata da uwa a gidan ko wanitsayayyen mafadi ko kuma kazamar uwa allah yabata gashi ne irin kanannadaddennan na fulani kobuzaye ko larabawa mai laushi mai santsin gaskebaki wullik mai tsawo sosai wanda yake taba doron bayanta. Amma me ? Yayi datti. Kura, amosalikai kace dambe tayi aka tumurmusa kan a cikinyashi . Sai wani kitso tuma tuma guda biyu dagagani ita tayi da kanta. Uwar biyu tace'' la la hannehaka kanki yake ? Amma kinyi wasa a yashi ko ?Gaki da gashi tubar kalla baki san yan mata yanzu ido rufe suke neman gashi ba. Da kudinsu ma siyasuke su kara yaya kika bar kanki haka babugyara ? Hanne tayi shiru kanta a sunkuye a kasatana kokarin daura dan kwalinta. Haisam wandayake zaune yayi shiru sai girgiza kai alamantausayi. Can ya nisa yace'' uwar biyu yanzu dai abunda za.a yi ga wannan wasu kudi ne ya sakecunkusowa daga aljihunsa ya mika mata tace'' nameye wannan kuma? Ya ce'' ina ganin hanne nabukatar abubuwa da yawa a kwana biyu da zatayigidanki . Ki tsaya a aishalle super market kitattambayi masu wajen irin man wanke gashi, dana kitso da sabulun wanka, wanki, abun goge kafa kisiya mata silifas. Ki duba kan idan akwaikwarkwata ki sayi shaltos duk a fesa su mutu. Kozaki taho aiki gobe to ki sami wata ki biya ta waccezata gyara mata kannan tayi mata kitso. Kai harmawanka kuyi mata da kanku ai bata wuce ayi mata wankan bama'' uwar biyu tace'' in allah yaso yaudin nan kafin mu kwanta da kaina zan gyaratagobe kuma ko zan taho aiki da diyata halima tananan auren ya mutu tana gida sai in barta da ita.Kuma ta iya kitso kala kala sana'arta kenan ki agarin da tayi aure'' haisam yace to nima gobe wajen karfe biyu idan an tashi a makaranta akwai tela dazamu je dashi can gidan naki ya auno ta zai dinkamata kayan makaranta(uniform)sai ki kwatantamin gidanki don naje. A kanti kike ko cikin gari ?Uwar biyu tace'' ah a cikin gari nake. Idan kajefada, kofar gidan sarki daga hannunkan a dama zaka ga titi ya mike to kabi shi kace a nuna makagidan dalhatun kazaure alhaji hamisu to lyngun mudaya ko a gidan kace gidan uwar biyu kake nemayaro karami zai nuna maka dan mu muke yi mususurfe, katangar gidanmu daya'' haisam yace'' toshike nan yanzu k dauki wannan kayan ku kai store din kicin ki ajiye su sai nan da kwana biyuidan anyo siyayya sai a dauko a zuba, sannankuma abinda nake so dake bana son ki gayawasauran abokan aikin ki ga dalilin da yasa zata jegidanki da sauransu. Ko a cikin gari ma kiyi gum dabakinki kinsan jama.a da surutu za.a yi ta cewa an kawo yar kauye makaranta babu komai sai dauwar biyu takai gidanta wani malami ne yayi matasiyayya da dai sauransu. Ba wai nace kin cikasurutu ba ko gulma a'a ko mutum daya yaji saidubu sunji. Kuma ai akwai matan kicin da yawa damuke gaisawa amma dana ga alamun suna da yawan magana ai ban kira su na basu amana bako ? To yadda tasa nace ta kira uwar biyu'' uwarbiyu ta kyalkyale da dariya dadi ya lullubeta '' tacehakane malam haisam ni dana ke cikinsu yangulma ko sun tambayeni ni nasan me zn fadamusu'' haisam yace'' yauwa ku dauki akwati da bokiti da katifar kamar yadda nace akai store aajiye, sai da safe'' suka ce allah ya kaimu''uwar biyuta kama akwati ta dora akan hanne ta dauki bokiti,da katifa a daya hannun suka doshi store din kicininda suma suke boye shirginsu . Malam haisamkuma ya rataya jakarsa ya nufi gidajen malamai (staff qurters). Zuciyarsa cike da tausayin yaddarayuwar hanne take. Kuma da burin canza matanan gaba* * * * HAISAM ABDULHAMID ZAKAR Sunanmahaifinsa ne abdulhamid zakar. Mahaifiyarsakuma sunanta NANA HAUWA'U Wacce a yanzu akafi saninta da hajiya nana ko kuma barista nana kasancewarta kwararriyar lauya ce. Mahaifinhaisam haifaffun unguwar kwalli ne a kano. Kumasun fito daga tushe daya yar kanwace aka hadasuaure a lokacin alhaji abdulhamid ya gama karatumdigiri dinsa a london yana da shekaru ashirin dabakwai ita kuma hajiya nana ta gama karatun sakandire tana da shekara goma sha shida.Dukkaninsu iyayensu suna da matukar arziki. Donhaka an sakar musu kudi yadda ya kamata antafka musu kerarren gida, motoci an kuma bawaalhaji abdulhamid jari mai tsoka yana juyawa itakuma hajiya nana ta fara karatunta na law a jami'a bayero ta kano. Allah ya albarkacesu da ya'yahudu, uku maza mace daya itace autar. Wacce ahalin yanxu ko yaye ta ba ayi ba karama ce.Babban shine yaya habib yanzu yana da shekaratalatin , mai binsa shine abdulhamid ake kiransa dahaisam yanzu yana shekararsa ashirin da shida mai binsa iziddeen shekarunsa ashirin da uku. Sai daiziddeen ya gama sakandire ya shiga jama'asannan aka yi masa kanwa mai shekara daya anakiranta da amratu.Girma yazowa alhaji abdulhamid da matarsaamma kumakarfi ya tasamma ya'yansa zasu iya kula da dimbindukiyarsada kamfanoninsa yaya habib ya kammala digirinsaa jamia'ar a.b.u ya karanta business admin a yanzu yana aikia kamfaninbabansa shine kuma mai zurga zurga zuwakasashe dabandaban na shige da fice da kayan kamfanonin.Haisam wanda a shekarar nan ya kammala karatun jami'a yakaranta bscgeography yanzu yana bautar kasa a f.g.g.ckazaure da zararya gama kujerarsa ta aiki nanan na jiransa a dayadaga cikin kamfanonin mahaifinsa. Na uku wato izziddenyana shekara tauku (level 3)a jami'ar bayero ta kano yana karatunlaw don yagaji mahaifiyarsa wato barista nana wacce itacebabbar lauyar kamfanonin . Tana kuma farin cikin ganin dayadaga cikin'ya'yanta ya taso gadan gadan da karatun lawwanda a cikin'yan shekaru kalilan zai gama ya zama cikakkenlauya ya canjeta alhaji abdulhamid ya dankawa yaya habibragamaraiki ya koma gida ya zauna yana hutawa sai daiyajekamfanonin fisha yaga yadda aiki yake tafiya yakoma gida.Dan lelen abba da umma wato haisam shine yafikowashagwaba a gidansu ko kuma nace shi akafishagwabawa tunyana kankani. Amma ai izidden ne yakamata yayishagwaba kasancewarsa ya dade yana auta kafin ayi masakanwa ammashi yana gefe tun suna yara haisam ne a kancinyarsabodatsananin biyayya, ladabi , tausayi da jinkai irin nahaisam shine ya kara masa fada a wajen mahaifansa sunfisha'awarsu zauna suyi hira da haisam sau dubu da suyi fayayansahabib tun suna yara saboda haisam yake magana acikin nutsuwa yake kalamansa masu muhimmanci akoda yaushefuskarsa cike da annuri(fara'a),wasa da dariya damanya dayara. Bashi da raini ga hakuri , baya ga zunzurutunkokari da allah ya bashi a bangaren karatunsa dukka akur'ani da bokonyasan alkur'ani kamar me a kansa duk gidansubabu maiiliminsa. Hatta mahaifinsa yakan yi masa tambayoyiakan duk wata matsalarsu ta addini ko ta zamani, yana datsananinhakuri sau tari ana masa abu da yawa yayi hakuri.Ammakuma duk gidansu babu mai zuciya kamarsa idanaka kureshi, idan yayi fushi abin babu kyau mai hakuri bai iyabacin rai ba.Da farko a enugu state aka turashi bautar kasa(n.y.s.c) kasancewar shakuwa da sabon da mahaifinsasuka yi dashi basa so yayi musu nisa don haka alhaji abdulhamidyasa adawo dashi kurkusa saboda yasan manya manyakasar nandaga yan boko har rukakkun yan kasuwa. Ammaduk da haka haisam yana korafi shifa kazaure yayi nisa da kanoa dawodashi cikin kano inda kullum zaina kwana gida, dakyar dai akalallasheshi yayi hakuri duka duka bazai yi shekaradaya ba zai gama ya dawo gida gaba daya. Don haka dukjuma'a yaketafiya gida wani lokaci ma a kanon yake yin sallarjuma'a sailahadi da yamma ake dawo wa dashi. Gashi yanzuma baifi saura wata uku ba ya kare bautar kasa kwatakwata ma yakoma daya ke muradi.Bayan tafiyar hanne gidan uwar biyu da kwanauku wato ranar laraba da sassafe sai ga wata mota an kawo hannemakarantahaisam ya roki wani abokinsa safiyanu yaje cangidan uwarbiyu ya dauko hanne da kayanta ya kawotamakaranta. Haisam ya gama mata siyayyarta kakaf ko yaranattajiranmakarantar baza su fita kaya ba(provision)kayanmakarantarta (uniform)suma har kala kala bibiyuyayi matatakalma kuwa kala kala akwai kito, sandal , kambos fari dabaki tsadaddu, silifas dan madina har biyu, ya suyomata dawasu yan kanti riga da siket suma kala biyu. Yasuyo matajakar zuba kaya mai kyan gaske yar madaidaiciya wato (travelling bag)a ciki aka zubawa hanne kayansawarta, nata nada kuwa yana gidan uwar biyu, kayan tande tandedamakulashe kuwa abun baya lissafuwa kama daga biskit kalakala, alewa (chocolate)indomie, madara, milo,sugar ,complakes da dai sauransu ko gari babuballe wanikanzo irin na yan makaranta makilin da brushhadaddu, mayukan shafawa da sabulansu masu kamshi gamayukangashi cike a akwatin hanne hankar da kaya allahya taimaketasa kansilansu ya tashi kawo maya akwatin yakawo mata randimemiya, mai cin kaya da yawa.Hanne sanye take da kayan makaranta(uniform)kafar ta kumafarin kambos ne da farar safa an tufke kitson kantada waniribom mai kyau mai fulawa, duk wanda yaga hanne kwanakibiyu da suka wuce a yau dai bazai gane taba tayifari kyalkamar yar larabawa, ashe mai dangwali ya ba neda bakinkwalli suka cabe mata fuska tayi baki kirin. Safiyanu yazobakin offishin malamai ya tsaya da motarsa sannanya fitodaga ciki ya juya ya kalli hanne wacce ke zaune abaya tanakokawa da murfin kofa ta kasa budewa abunka fa bakauyiiya.Wannan ne karo na farko da hanne ta taba hawadon hakabata san ina zata ja kofa ta bude ba. Safiyanu yazagayo dasauri ya bude mata, ta fito yace'' to dauko jakar litattafan nakimana'' hanne tasa hannu ta jawo wata bakar jaka(schoolbag)tsadadda mai kyan gaske, yar madaidaiciyadaidaibayanta cike take da kitattafan rubutu da litattafan karatu(textbook)duk dai kamar yadda aka zano ajikintakardar babuwanda haisam bai siya mata ba ga biruka da fensirdamathematical set din su ya suya mata . Safiyanu ya nunawahanne yadda zaya rinka ratayawa a bayanta tarataya sukanufi cikin ofishin. Suna shiga suka iske wani malamibayansafiyanu ya mika masa hannu sun gaisa sai yayi masa bayaninabunda ke tafe dasu yace daliba ya kawo, sai yanuna masaofishin vice principal yace nan zasu shiga.sukayi sallama suka shiga suka iske viceprincipal yanaharhada wasu takardu a gabansa, bayan syn gaisasafiyanu yashaida masa cewa yarinya ya kawo yar aji daya cesabuwar zuwa sai ya nemi daya bashi takardar shaidar cewaita dalibarnan makarantar ce wato (joining instruction)daman haisam yabashi ya dauko ya mika masa ya duba yace''sunanta hanne habu imamu daga babban mutum ko ? Safiyanuyace ''eh,''vice principal din nan ya kurawa hanne ido yanakallozuciyarsa cike da mamaki ga yarinya kyakykyawakamar baturiya gashin kanta har baya amma duk dama antufkemata da ribon amma kuma sunnan kauyawagareta gata kumadaa kauye. Ya ce a ransa'' wata kila dai asalin garinsune babban mutum din amma daga birni take, can yanisa yace''babu komai,'' ya jawo wani littafin rasitai ya budeyace dasafiyanu'' sai ku bibbiya kudaden in baku rasitai dasauri don yanxu lokaacin assembly ne, don taje ta shiga cikindalibai ayida ita. Vice principal ya lissafawa safiyanu yawankudade dazai kawo safiyanu ya dauko ya bashi, shi kumayana rubuta rasitai har ya biya kudin komai ya ce '' sannan yafadi sunandakin da zata je, sannan zata je j.s.s. 1A ajin malamhaisamsunan ajin, yanzu ka kaita hall ayi assembly da ita,kayanta kuma a barsu a nan bakin staff room ana tashi tazozamu samaigadi da prefect din dakin suje ta bata gado.Safiyanu ya ce''to'' yayi godiya suka fito yana sake yiwa hannebayani akan abinda vice principal ya ce, yana kuma karalallashinta ganinyadda nan da nan ta canja hankalinta yayimummunan tashidaga shigar su ofishin vice principal duk kwalla tacika mata ido saura kiris ta fashe da kuka. Yace mata'' kar kiyikuka nanmakaranta ce karatu kawai za.a koya miki babumai zaginkiballe duka kinji. Gashi ajin malam haisam za,a kai kidon haka baki da matsala zai kula dake''suna tsaye a bakin baranda yana yi mata nasihasaiga viceprincipal ya fito daga ofishinsa zai tafi hall wajenassemblyyace'' ah har yanzu bata tafi assembly ba ai gara kuyi sallamata tafi,'' safiyanu yace '' aima shikenan mun gamadaman halldin zan tambaya don bamu ganshi ba,'' viceprincipal t harcikin hall din yashige da hanne a lokacin principal tana bayanihall din yayi tsit kowa yana sauraro. Amma dagashigowarhanne da vice principal sai kowa hankalinsa yakoma ga kallonhanne. Hanne ta zama yarinya ''yar dagwas 'yar karama maikyan gaske akwai dubbunan dalibai a makarantardaga jahohidaban daban amma babu mai kyawun hanne watokamarwata tauraruwa ce mai haske a cikin taurari. Sai sheki take danfarar fatarta hanci har baka, dan karamin baki,gazar gazargashin gira dana ido fatar jikinta luwai luwai irintayan hutuamma ita dai daga innallahi. Ga ido dara dara bata da kibakuma bata cika tsaho sosai ba gata dirarriya duk dadaikarama ce masassakin budurci bai fara sassakataba. Wasukitso ne yiri yiri aka yarfa mata kamar bada hannu aka yisuba. Hanne tayi kyau kwarai da gaske a cikinkayanmakarantar nan ga 'yar jakar litattafanta a baya.Babu wandazai kalli hanne bai sake juyowa ya kalli halittar ubangiji ba.Dalibai manyansu da yaransu babu wacce bata cedama nicewannan ba ko kuma ace 'yata ce a ransu ba. Hattahaisamwanda ke tsaye a bakin kofa bai gane hanne ba. Suka zo sukawuce ta gabansa ya bita da kallo sai dai a zuciyarsayaketambayar kansa da kansa ina nasan wannanyarinyar?Tabbasa na santa a wani waje, sai daga baya zuciya ta bashiamsar cewa wannan itace hanne habu kenan. Yayimatukarmamaki ganin yadda hanne ta koma haka a kwanabiyu,hanne ta tsorata ta kuma rikirkice ganin dubbunnan idanuwacaa a kanta, ta tsaya cak, ta kasa tafiya tana shirinfashewa dakuka.Vice principal yayi kiran wata prefect dake tsaye agefe yace tazo ta kaita layin 'yan j,s,s 1A. Tazo ta kamahannun hanne takaita layin ajinsu ana ci gaba da assembly kamaryadda sukasaba. Bayan principal ta gama jawabinta, viceprincipal ma ya fadi albarkacin bakinsa sai aka nemi sauranmalamai sucewani abu akan dokar makaranta. Bayan sun gamaaka yinatsonal pledge kowa ya kama gabansa, ya nufiajinsu. Hanne ta tsaya cak a inda take tsaye tana kallon dalibaikowa yanatafiya ajinsa ta rasa ina zata nufa. Haisam ya matsokusa da itaya ce'' hanne yaya kika tsaya bakya gani kowa yanufi ajinsu ke kika tsaya idan baki sani ba, ba sai ki tambaya ba.To nanmakaranta ce kowa ta kansa yake, gara ki rinkatambayar dukabinda baki sani ba, muje in nuna miki ajinnaku, hanne tace'' to'' ta bishi suka doshi bangaren da ajujuwa sukeyaci gaba dayi mata nasihohi akan kada ta sake ta zamawawuya, idan bahaka ba sai sauran dalibai su raina mata wayo tazama duk abunda bata sani ba ta tambaya musamman idanmalamiyana darasi idan bata ganeba tayi masa tambaya.Hanne nasauraro da alama kuma nasihohin suna shigarta.Haisam ya kalleta yayi dariya ya ce'' hanne ince kin zamacikakkiyardaliba babu wannan damarar? Hanne ta kyalkyaleda dariyahaisam yace'' to tunda kin zama yar birni 'yar bokomai aji to yanzu komai naki yzai koma na aji, kin san abundanake nufi?Hanne tace ''a'a'' yace to sunanki zai tashi dagaHANNE HABUIMAMU ZAI KOMA HANNAH ABUBAKAR IMAM.kowaya tambayeki sunanki kice..'' kafin ya fada cikin murnada farinciki tace '' hannah abubakar imam'' haisam yatuntsire dadariya yace harma kin rike sunan kenan? Hannetace eh hannah yafi dadi Allah'' a daidai wannan lokacisuka haubarandar ajin haisam ya wuce gaba ya shiga ajinhannah nabiye dashi a bayasuka shiga dukkan daliban ajin suka mike dongirmama malaminsu suka hada baki dukkansu''good morning sir'' haisam yayi murmushi yace''morning how are you ? Suka sake hada bakisuka ce'' we are fine sir'' yace thank you sit down ''kowacce ta zauna akan kujerarta. Haisam ya jawo hannah gaban aji yace'' ga wata sabuwar dalibakun samu'' rauda itace monita ta mike tace'' lah ,what is your name ? Hannah ta daga ido tanakallon haisam'' ya harareta ma'ana ta bada amsa ,hannah tace'' my name is hannah abubakar imam''kama yadda haisam yace ta dinga fada. Nusaiba wacce itace mataimakiyan monita tace'' emh, nicename you are welcome hannah'' haisam yayimurmushi ya ce'' kun fara iyayin naku ko ? To mazaku saka mata kujerarta a tsakiyar taku a gabakuma kunga itama yar kucila ce kamar ku'' cikinsauri rauda taje bayan aji ta dauko kujera ta kawo ta koma ta dauko tebur yazo ta dasa a tsakiyar su ajere. Dake duk ajin su duka ukun sune kanananajin sunfi kowa kankanta kasancewar akwaidingin dingin din yammata a ajin musammankabilun na wata sai ka rantse uwa ce amma yar ajidaya ce farin ciki ya lullube hannah da haisam musamman ma haisam yaga hannah ta samu shigaa wajen nusaiba da rauda wadanda su suka fi dukyan ajin kokari dan rauda a america tayi karatunnusery da primary dinta don haka tana bala'inkokari ga turanci daya kama bakinta hausa matana kokarin ta subuce mata.Kuma auwal abokin haisam ne na kuttan kaibabanta alhaji shitu abokin baban haisam nesannan ramla yayarta ita haisam zai aura don hakanema aka kawo rauda makarantar saboda haisamyana nan tazo akayi mata jarabawa taci shikenanaka dauketa, don haka nema take kiransa da yaya haisam sabanin uncle haisam da sauran dalibaisuke kiransa. Nusaiba ma wata tsadaddiyarmakaranta ta gama a abuja, ita yanzu hakaiyayenta suna abuja karatu ya kawota nan ammasu haifaffun garin gwambe ne fulani, rauda danusaiba sun zama kawaye tun ranan da suka hadu ranar da aka kawosu makaranta, ajinsu daya sukakuma ci sa.a dakinsu daya don haka ga gadonrauda ga na nusaiba kuma sun hada kayanakwatinsu. Haisam yace monita da mataimakiyartaku biyoni waje ina da magana daku rauda danusaiba suka mike suka bi haisam wajen ajin. Hannah na zaune babu abunda take sai kallonginin ajin da dalibai daya bayan daya taga kowaccesanye da uniform dinta tsaf tsaf, fararen takalmakambas da fararen safa kan kowacce kitso ne tar.Hannah tace a ranta ashe da na sha kunya da aceranar da baba ya kawo ni a haka na shigo ajin nan da na fita daban, kai wannan malami ya taimakeniallah yayi masa albarka. Taci gaba da kallon gininajin da irin zane zane da akayi a takarda duk anlillika a jikin bango ga fankoki a jikin silin sunatafitar da sansanyar iska suka , ginin bulo hannah tafada a fili ba tare data san a baiyane ta fada ba, bayan fitarsu haisam a bayan ajin suka tsaya yakalli rauda ya juya ya kalli nusaiba yace raudanusaiba su duka suka amsa yaci gaba da cewa gahannah nan , kamar rauda kike kawar nusaiba tohannah ta zama kawarki itama, sannan kamaryadda ke nusaiba kike kawar kawar rauda to ina son hannah ta zama kawarki duk da ku biyudakinku daya to hannah ma yar dakin kuce dakesafiyanu ya fada masa sunan dakin hannah yacedon haka ku uku dakinku daya ajinku daya. Kamaryadda a ko ina kuna tare a hall ne, a ajine a daki neto hannah ma ta zamana kuna tare itama kanwata ce kunji ko ? Su dukka suka amsa. Nusaiba tace''uncle haisam ko baka ce mu zama kawaye badaman zamu zama tana burgemu'' haisam yayidariya ya juya ya kalli rauda yace'' kanwata ke bakice komai ba ke bata burgeki ? Rauda ta tabe bakitace'' yaya haisam rannan fa kace nice kadai kanwarka a makarantar nan yanzu kuma kace itace'' haisam ya kyalkyale da dariya ya dafa kantayace!! Rauda kenan, ai har yanzu kina nan amatsayinki na kanwata itama hannah yar uwata cekibga dole kanwatace, nusaiba ma kanwata ce donhaka karki damu. Gata nan duk abunda bata sani ba akan karatu ki koya mata. Haka kuma maganada turanci ku rika tunasar da ita koda ta manta tayihausa karku rubuta sunanta a masu yin hausa sai ahankali zata saba itama ta rinka yin turanci sosai.Haka a daki idan bata san yadda zata yi amfani dawani abu ba kamar man gashi in zata shafa a jiki ku nuna mata mata na gashi ne ba ku ringa yi matadariya ba kuna gayawa kawayenku kunji ?Musamman ke rauda kinga rose suna yawan kawomun kararki wai kina yi musu tsawa kar in sakenaji kina yiwa hannah kinji ko ? Rauda tace''yayaya za'ayi ta shafa man gashi a jiki sai kace bakauyiya'' haisam ya ce a,a wai a misalai nakenufi, koda ace zata manta ta dauko man gashin''tafiyar wani malami ce tasa duka hankalinsu yahuya baya don ganin mai tahowa, haisam yace'' toshikenan ku koma aji ga malam shaiya nan zaikaya muku maths an kada firs period,'' suka ruga a guje, malam shaiya ya mikawa haisam hannu sukagaisa sannan ya nufi s.s.3c yana da period yanakoya musu geograpykamar haisam yayi duba da yace idan ta daukoman gashi zata shafa a jiki haka kuwa aka yihannah babu abunda ta sani a kayan akwatintadaga ta dauko man wanke gashi [shamppoo] takwaba a jikinta sai ta dauko man shafawa ta makaa kanta makilin ma wani lokaci a tsagar kitso rauda tazo ta isketa tana sharbawa. Suyi ta dariya har sugodewa allah daga karshe dai suyi mata bayanidalla dalla , wannan ne na kaza wannan kuma awaje kaza ake shafawa. Babu laifi a sati biyuhannah ta waye ta gane duk kayayyakin amfani nazamani sannan ta koyi cin kayan gwangwani dana kwali, don da farko inda suka dama comflask damadara cokali daya zatayi sai ta fita a guje ta kelayaamai bata sanshi ba haka sardine da gesha kifingwangwani sai taki ci tace tsutsace amma dagabaya duk ta waye tana ci. Hannah tana farin cikimatuka da wannan sabuwar rayuwar data tsinci kanta. Abinci lafiyayye a akwatinta na makaranta ,gashi tana cikin yara sa'anninta suyi karatu taresuyi wasa tare musamman nusaiba tana bala'inkaunar hannah tafi rauda kirki don rauda ta cikanuna isa da nuna tafi kowa kuma duk girmanka saita riga daka tsawa.Ta fannin karatu kuwa. Ada hannah dumama kujera take yi kawai saboda tsantsar turanci ake yia makarantar amma sai nusaiba ta lura hannahbata fahimta don haka a koda yaushe bayanmalami ya gama darasinsa sai ta matso da kujerartahar kusa da ta hannah tayi mata bayani dalla dalla. Haka shima malam haisam kullum a prep dinyamma yana zuwa ya kira hannah ya koya mataabubuwa da dama. A wata daya hannah ta faragane turanci fiye da yadda kuke zato. Ranar wataasabar da daddare ranar ne ake warewa dalibai sushakata su hole rayuwarsu kamar a saka musu kidan disko su cashe wasu kuma su kada tebur dakansu suna waka wasu na rawa. Wasu kumatalabijin ake kunnawa da bidiyo suyi kallon kasetduk dai abunda ransu keso shi zasu yi. Daga 'yanj.s.s 1 har manyansu s.s.3 Zaharaddeen Shomar Whatsapp 08168575100 GANGARJIKINSA NA AURA 1 Part 2 Posted by ANaM Dorayi on 02:02 PM, 30-Apr-15 Under: Gangarjikinsa ta Aura Wannan rana ita ake kirada '' social night'' uncle haisam kuma shine social master wato shine malamin da yake kula da dalibaiyake kula da c.d din da ake kunna disco da bidiyoda talabijin din da ake kunnawa. A wannan dare anyarjewa dalibai su saka kayansu na gida{persinal}kowane iri ne kama daga leshi ko shadda riga daskit kai har jeans da tea shirt duk zasu iya tsukewa. Rauda sarkin rawa ita har tunanin wannan asabardin wacce irin rawa zanyi don har fili ake batakowa ya koma gefe yana kallonta rawa salo salohar wasu suke kiranta janet jacson wai kanwarmacheal jacson nusaiba kuwa ita da hannaah babuabinda suka fi so irin kallon bidiyo hausa fim masu kyau malam haisam yake samowa ko nigerian fims.Social night din wannan asabar din bata yiwahannah da nusaiba dadi ba saboda bidiyo talalacebabu kallo sai dai c.d aka kunna aka ware kida dukmai bukata yaje ya cashe wasu na rawa wasukuma na gefe suna kallo. Amma wasu suna kan barandar wajen hall din a zazzaune basa sha'awaryin rawa ko kallon masu rawa kungiya kunkiyakowanne da group dinsu suna waje suna zazzaunesuna hirar duniya. Hannah da nusaiba suna dayadaga cikin wadanda basu shiga cikin hall din bawajen kida suna zazzaune a can kan wata barandar ofishin malami suna hirar duniya, hirarma ma jifa jifa suke yi saboda duk rayukansu abace yake yau babu kallo kuma wani hadaddenamerican film mai suna''mr bones''uncle haisamyayi musu alkawarin zai saka musu. Nusaiba tayiajiyar zuciya tace anya kuwa yau zan iya bacci saboda bakin ciki na kudiri niyar danin firm dinnan,wallahi fim din akwai abin dariya muna dashi fa agidanmu. Hannah tace na last week ma yayi kyauga abin dariya osofia in london yaya haisam ya iyazabo man films masu kyau. Wata murya ce abayansu tace na kamaku kuna gulmata'' suka juya da sauri sai suka ga yaya haisam ne su duka sukatuntsire da dariya ya zagayo suka matsa masa yashiga tsakiyarsu ya zauna yayi murmushi ya cekuna gulma ta ko, dan ban kunna muku kallo bako ? Nusaiba cikin shagwaba tace'' yaya haisam harkwalla nayi fa wallahi yau duk ranmu a bace yake. Haisam yayi dariya yace'' kai haba harda kwalla ?Ke fa hannah kema kinyi kukan ? Tayi murmushitace a.a banyi ba uncle haisam. ''yaci gaba da jansuda hira yana zolayarsu kamar yadda ya saba wasada dariya da dukkanin daliban makarantarmusamman da wadannan ukun. Ya ce dasu '' ga rauda can a hall tana cashewa kuje ku tayata manako kuma kuyi mata liki. Suka danyi dariya suka ce ''mu bama rawa'' suka ci gaba da jugum , haisam yalura yau dai nusaiba da hannah babu kanta basason magana balle doguwar hira yace nusaiba,hannah yaya haka kowacce tayi zugum babu nishadi kamar yau ba ranar social night ba. Nusaibatace''yaya haisam tsabar bakin cikin rashin kallonnan ne yake damunmu.'' yace shi yasa baku fara'a?To yanzu daya bayan daya sai kun yimin waka darawa tunda yau social night dole kuyi murna'' cikinshagwaba nusaiba tace''yaya ni bana iya waka ba sai dai hannah ta fara tunda itace karama. Hannahtayi dariya tace to bari inyi muku wakan sarkingarinmu,'' hannah ta fara tafi ta fara rero waka.Haisam yace'' to tsaya tafi akeyi muma mu dingatayaki muna muki amshi ? Tace'' ai da kwarya akekida dan dai babu kwaryar ne. Yasa hannu a aljihunsa ya zaro wannan abun busar daya karba awajenta ya ce zai ajiye mata ya ce'' ga abun busarkima ki busa mana ki rero mana wakar kiwo'' cikinfarin ciki hannah ta karbi abun busarta ta haujujjuyashi tana cewa'' allah sarki abun busata nadade ban busa kaba,'' nusaiba tace '' lah busa muji yadda akeyi'' hannah ta kaikaice ta fara busa abunbusarta tana rera waka kamar haka. muyi kiwosamari. Kuyi kiwo yan mata kiwo baiwa ne. Wakabaiwa ce. Haka busa ma baiwa ce kuyi soyayyasamari. Kuyi soyayya 'yan mata ke 'yar budurwaina naki gwanin ? Ni nawa gwanin baya nan. Yayi tafiya amma koda bana tare da gangar jikinsa.Ruhinsa yana tare dani. Haisam yace '' hannahtsaya meye koda gangar jikinsa bata tare daniruhinsa yana tare dani ''? Tayi shiru can tace ohonima haka ya mun wakar nusaiba tace meye ''ruhi ? Hannah tace '' nima ban sani ba, ina jin larabci ne , haisam yayi dariya ya ce '' yarinta mai dadi. Kwanci tashi yau kwanan hanna arba'in amakaranta har an kafe musu tine table dinjarabawa wato end of 1st teem examinationkasancewar daman dalibai sai da suka yi kimaninwata guda da dawowa makaranta sannan akakawi hannah babu abunda yaya haisam yake yi sai nasihohi da yake yiwa yan ajinsa wato j.s.s 1a dakowacce ta cire wasa tasa littafin karatu a gabantadon suci jarabawa. Haka kuma wasu lokuta ya kankira kannansa rauda, nusaiba da hannah yanakara musu fada dasu dage sufi kowa cin jarabawaya sake xewa'' hannah bana jin fargabar su rauda kamar ke don haka ki dage duk abunda ba ki saniba ki tambayi nusaiba ko rauda idan sun sani sukoya muki, idan kuwa basu sani ba to kuzo kutambayeni. Haisam yayi musu rantsuwa da allah acikin su ukun nan duk wanda ta fadi jarabawartasai yayi mata bulala kuma daga ranar data fadi jarabawa babu ruwansa da ita ya cireta a cikinkannansa gaban hanna ya fadi rasa dajin bayaninyaya haisam tace a ranta tace idan yaya haisa yacebabu ruwansa dani aina shiga uku tunda babu maiyimun siyayyar makaranta karshenta ma karshenkaratuna yazo. Ta kudiri aniyar daga yau babu ita babu cikakken bacci zata dage da karatu don tacijarabawa kada haisam yayi fushi da ita. a sati dayasu hannah suka gama jarabawarsu,jarabawabibiyu suke a rana daya. Don haka babu hutu badare ba rana kowacce ta dukufa da karatu,musamman hannah sallah ce da cin abinci tashinta daga kan littafin karatunta, haka kuma ta zanajarabawar cikin sauki ma'ana da an bata questionpaper sai taga tasan amsoshin gaba daya, hakatake amsasu cikin sauki saboda tsaban ta gamakarance litattafanta, hannah tasan yaya haisamzayyi murna da sakamakon jarabawarta tunda tayi karatu yadda ya kamata. Hutu kuma sai juma.a donhaka dukka wadannan ranakun babu abinda sukeyi sai wasanni da raye raye da wasanninkwaikwayo na kungiyoyi (club)din makarantarkasancewar akwai kungiyoyi daban daban amakarantar kaar english club, hausa club, jet club. Che,ical club, geography club. Yoroba da igbo dadai sauransu, kuma kowacce daliba daga yar ajidaya zuwa shida tana da damar da zata shigakowanne club a makarantar. Su kuwa malamaicikin satin nan suka dukufa da aikin makinjarabawar dalibai, don ganin kafin ranar hutu sun bawa kowacce daliba sakamakon jarabawarta tatafi dashi gida iyayenta su gani. Ranar alhamis anagobe hutu haisam ya tara 'yan ajinsa a bakinbabban dakin taron dake makaranatar wato halldon ya bawa kowacce sakamakon jarabawarta(report card) 'yan ajin malam haisam suna da dimbun yawa don dalibai saba'in da shida ne a ajinhausawa da yarbawa,igbo,musulmai da kiristocisma da talatin ba hausawa bane kuma ba kiristocibane, wata ko zo bata sani ba da hausa, tundadaga kudu suke babu abunda suka sa a gaba saikaratun littafinsu don shine abunda ya kawosu tun daga uwa duniya zuwa nan arewa. Don haka babukoma baya a ciki kowacce tayi iya kokarintamatuka a wannan jarabawa. haisam ya kallifuskokinsu daya bayan daya sannan ya kyalkyaleda dariya. Abun mamaki babu wacce ta taya shidariya kamar yadda suke wasa da dariya a aji yau kowacce fargaban jin sakamakonta takemasamman ma hanna. Tunanin maganar da yayahaisam ya fada yayi musu ranstuwa yace dukwacce ta fadi jarabawa sai yayi mata bulala kumababu ruwansa da ita. Hakika bata fargabar bulalarsosai tafi fargabar babu ruwansa da ita din daya fada, idan haisam ya cire hannunsa akan hannahwaye kuma ya tsaya mata a duniya yadda takekaunar makarantar nan aiko hutu bata so ayi. Watohannah na daya daga cikin yan kwaleji tafi gidadadi, ga uwa uba kwanciyar hankali wasa dadariya da kawayenta sabanin a gidansu sai bauta. Anan makaranta akan sasu aiki ko aike ammabamai wahala ba kasancewarsu kanana 'yan ajidaya dole seniors zasu aikesu. Haisam yace ''oh''yau babu dariya duk kunyi cirko cirko kuna jiransakamako to da yawa daga cikinku kunyi kokariamma wasu basu yi kokari ba don haka wadanda basuyi kokari ba sai sun dage idan ba haka bakarshen shekara za'ayi musu repeating kowa yawuce aji biyu a barku a aji daya ku sake maimaitashekara,. Gaban hannah ya sake fadi ras sai addu'atake sannan taji dan saukin dukan da zuciyartatake yi mata. Haisam yace'' yanxu zan fara kiran sunan wadanda suka yi na daya zuwa uku sai atafa musu zan basu kuma kyaututtuka sannan nakirawo na hudu zuwa goma zuma zasu fito a tafamusu sune suka fi yin kokari sauran kuma sai kudage nan gaba ''hadiyar yawu yake ji mukut mukutdakiban nayi don faduwar gaba dariya ta sake kecewa malam haisam ya girgiza kai , sannan yabude file din dake hannunsa yace'' dalibar datayimatukat kokari ta zo ta daya itace Rauda shitu muktar ta kwalla kara don dadisauran suka sa tafi suka juyo suna mata kallonsha'awa kowacce a ranta tana dama nice raudashitu a ransu haisam ya ce taso'' fuskarta cike dafara'a zuciyarta cikw da farin ciki tazo ta tsaya agefen haisam yaci gaba da cewa, sai kuma wacce tazo na biyu itace nusaiba idris,'' farin ciki ya lullubenusaiba itama tazo kusa da rauda shitu ta tsayadalibai nayi mata tafi raf raf, ta uku kuma itacepamella matin benin,pamella ta daka tsalle danmurna ana tafa mata itama ta fito ta tsaya kusa danusaiba idris'' hannah na lungu ta kankame guiwarta da hannayenta ta zura kanata a matsematsin cinyoyinta yayin da kuka ya kece mata.Taga kawayenta biyu rauda da nusaiba wadandasuke karatu tare sun zo sun fita kokari . Ta gamasaddakarwa yaya haisam ya cire hannunsa dagakanta tinda batayi kokari ba. Haisam ya rufe file din dake hannunsa ya kalli sauran daliban da sukezazzaune a kasa yace'' kunda wadannan ukunsunfi kowa kokari a ajina don haka zan basukyaututtuka da zasu je gida su nunawa iyayensusuji dadi , bawai su daban suke daku ba a.a kumakowacce a cikinku ta dage zata iya zuwa na daya, biyu da uku. Don haka duk wacce take so itamanext term taji sunanta a cikin wadannan ukun to tadage da karatu. Don haka to ku sake tafawarauda,nusaiba da kuma pamella. Tafi raf raf raf yadinga tashi saida haisam yace ya isa tukunna sukadaina. Ya dauko wata katuwar anbulan wacce aka like ta da salataf an yi rubutu da maka dara darakamar haka. FIRST POSITION IN J.S.S 1A RAUDASHITU MUKTAR ya mikawa rauda , daliban suna tafamata raf raf yace taje ta zauna, ya sake dauko watawacce girmanta bai kai girman na rauda va, itamaan like jikinta da salataf an rubuta SECONG POSITION IN J.S.S 1A NUSAIBA IDRIS Ya mikawa nusaiba akatafa mata ta tafi ta zauna itama. Ya dauki ta karshenitama girmanta bai kai ta nusaiba ba, ajikinta anrubuta. THIRD POSITION IN J.S.S 1A PAMELLAMARTINS BENIN Aka tafa ta karba da murna ta tafita zauna, haisam yace''to yanxu san kira na hudu zuwa goma suma su fito nan su tsaya a tafa musudon suma sunyi kokari matuka.'' fargaba ta sakedira a zuciyar hannah. Tace a ranta' idan kumabana cikin mtane goman nan ni kaina nasan banyikokari ba, shi kenan karshen makaranta na yazodon nasan tunda malam haisam ya rantse nasan da gaske yake sai ya zaneni sannan ya korani gida, tarushe da kuka dan ta tsani wannan kalman ta gidasaboda tsananin da ake yi mata da azabtarwa .Baya ga bautuwa ga horon yunwa, babu wankako tayi wankan ma kusan daya ne da batayiba,don wankan babu sabulu, sai wani lokacine idan tayi wanke wanke dan omo yayi saura takeboyewa tayi wankan dashi shima a sati baifi sodaya ba anan kuwa sunkinan sabulu zesr haisamya siya mata, ga mayukan shafawa iri iri ba kalarkitson bane ko tayi kitsin kwana biyu ya farazamewa . Amma yanzu da ta sami mayuka masu sashi yayi laushi sai take wankewa da man wankegashi ta mulke da man gashi tasa ribon ta dauretamkar indiya baki sidik a kwance fatar jikinta tayiluf luf sumul sumul ba ita ba, ita bata ki har shekarashida ba'a yi hutu ba . Malam haisam yaci gaba dakiran daliba ta hudu, ya kira ta biyar, ta shida hannah bata ji sunanta ba, ya kira bakwai da tatakwas. Sai kukan da take ya kara tsananta har nakusa da ita suka fara jiyo sheshshekar kukan datake yi suna juyowa suna kallonta, haisam ya kirata tara sannan ta goma yace '' hannah abubakarimam . Shima sai yayi ajiyar zuciyar jin dadi hannah ta mike ta taho idonta tamkar anyi wasan ruwakaca kaca da hawaye. Haisam ya dafa kanta yacehannah kukan meye kike shashsheka lafiya ? Yishiru goge hawayenki kinzo na goma kinyi kokari''dadi da kwanciyar hankali suka lullube hannahyasa aka dinga tafa wa daliban da suka zo na hudu zuwa na goma. Daga karshe yace su koma suzauna yaci gaba da kiran dalibar data na goma shadaya zuwa saba'in da shida ta karshen kenan watagandamemiyar ajin ce tafi kowacce girma a ajin maisuna eneka eddiward itace tazo musu ta karshe, dayawan dalibai suka rushe da kuka jin malam haisam ya furta repeating suna tunanin shikenanza,ayi musu repeating haisam ya shiga lallashinsuyana cewa kowa tayi kokari babu wacce za.ayiwarepeating kasancewar da damar da zasu iyadagewa nan gaba ba.ayi second term ba balle thirdterm sannan suka ji dan sanyi a ransu suka fara goge hawayen daya jika musu ido. Hannah takoma gefe tana kallon jifgin mutanen data kayaryayin da zuciyarta take jinjina mata ai kinyi matukarkokari tunda kin wuce mutane sittin da shida, farinciki ya lullube zuciyar hannah. Ta sake sa randawowa makaranta idan hutunsu ya kare kasancewar taji haisam ya yaba da sakamakontadon haka zai sake yi mata siyayyar makaranta dabiyan kudin makaranta da aka ce duk term akebiya kuma dubunnan nerori. bayan kowacce tayishiru da kukan da dayawa suke yi sai haisam yace''duk kunyi kokari kasancewar 'yan ajin babu marar kokari yace kowacce tazo ta karshe anan ajin ne ab.c. Ko d ita zata zo musu ta wajen goma sha waniabu, kunga kowacce tayi kokari karku damu. Yadauko wata katuwar leda a gefensa ya ce dai dai suringa tasowa suna karba.Biscuit nemai dadi ya rarraba musu kowacce daliba ta samutun daa kan rauda har eneka eddiward kowacce tafara murnar tayi kokari. Da haisam yaga duk sunware yana musu wasa da dariya sai yace'' ina si na shaida muku daga yau ko kuma ince daga dagagobe ranar hutu idan na tafi hutunnan shikenan natafi kenan. Gaban kowacce ya yanke ya fadi. Bamugane ka tafi ba kenan uncle haisam '' su duka sukatambaya . Haisam yayi murmushi yace ''kun san nicopper ne. Nazo ne yin bautar kasa wannan makarantar(N.Y.S.C)KUMA yanxu lokaci yayi damuka kare don haka idan na tafi hutun nan bazandawo makarantar nan ba. Ina muku fatan alherikuma shawara nake baku akan kowacce ta dagetayi karatu banda wasa '' kowacce jikinta yayi sanyifuskarsu alamar basu ji dadin wannan batu na class master dinsu ba . Suna son haisam saboda kula dasoyayya da yake nuna musu wasa da dariya akoda yaushe sai wasu dayawa daga cikinsu sukarushe da kuka. Babu kamar rauda, nusaiba dahannah, ai kuma gara rauda da nusaiba akanhannah wani sabon tashin hankali ya rufta mata fiye dana dazu. Haisam zai bar makarantar nan itakuma ina zata dosa ?''.Haisam ma wani tsananin bakin ciki ne yamamaye a zuciyarsa yana tsananin son yan ajinsa.Baya so ya tafi ya barsu yana tausayinsukasancewar yan yara babu kuma wani malami komanyan daliban da zasu zauna suna basushawarwari kamar hannah, wa zai kula da hannah? A bar zancen kudin makaranta da siyayya(provision )ita kanta tana bukatar a kula da ita dakara karfafa mata gwiwa wajen idan ta tafi hutugida ta dawo makaranta. Koda a gida an ce baza tadawo ba tasa kuka har sai an dawo da ita. Ga wasuabubuwa da suka yi mata nauyi a aji ma'ana bata ganewa sai shi haisam da kansa yake nunnunamata har sai ta gane. Allah sarki hannah ya fada azuciyarsa ji yake kamar ya rushe da kuka dantsananin bakin cikin rabuwa da dalibansa. Ammaya daure ya dinga lallashinsu, idan wadannnansuka yi shiru sai wadansu su rushe da kuka. Haisam har ya gaji da lallashi yace su tashi su tafidakunansu sai gobe zasu hadu a wajen assemblyhutu, suka nufi dakunansu kowacce na sharbehawaye. Haisam kuma ya nufi gidansa dake staffqurters yana mai matukar jin ba dadi a ransa. Kowayayi shiru ya daina kuka amma banda hannah. Nusaiba da rauda suka dinga lallashinta amma takidainawa taki cin abinci sai tayi kamar tayi shiru tadaina sai ta tuna ta rushe da kuka. Haka ta yini curtana kuka. Rauda tace waini hannah kukan nan dakike yi kinfi kowa son yaya haisam ne ? Ni fa munfikusa da shi babana abokin babansa ne. Kuma yayana auwal abokinsa ne. Haka kuma yata ywadaya uba daya ramla budurwarsa ce koma nacematarsa ce don har ansa musu raba, sanda mukeamerica yan gidansu a gidanmu suke sauka insunje kuma da muka dawo nan kasar saboda yayahaisam ma aka kawoni makarantar nan tunda yana malami yace da abbana makarantar akwai karatu.To harni na hakura na daina kuka ke ba za kihakura ba kamar kinfi kowa sonsa. Ya ce dai kekanwarsa ce kuma ni a sanina 'yan uwansa duk akano suke na sansu kuma amma ni ban sanki ba.Kuma duk yan uwansa babu masu kama dake ke kamar balaraniya kike ko buzuwa ce ni ban saniba'' nusaiba tace'' haba rauda meye haka in ba yaruwarsa bace zai fada ne ? Hannah ta sake rushewada kuka. Daman abunda rauda take yi mata yaisheta. Tunda aka kawo ta malam haisam yacekanwarsa ce taga rauda tana kishi da ita. Wai ya za ayi ace hannah kanwar yaya haisam ce bayan itakadai ce kanwarsa a makarantar. washe gari da sassafe dalibai suka shirya kayansutsaf na tafiya gida suka saka kayan makaranatar(uniform) suka dunguma babban dakin taro (hall)don yin assembly hutu. Hannah nusaiba sukakinkimo jakunkunan kayansu na sakawa sukakuma rarrataya jakar litattafansu a baya. Akwatinsu kuwa da katifu da bokitai a wani daki ake lufgawaa rufe. Ba.a tafiya dasy gida. A bakin hall din sukaajiye jakunkunan sannan suka shiga cikin hall dindan yin assembly. Kallo daya haisam yayi wahannah yasan tasha kuka kuma tana cikin tashinhankali . Principal ta sanarwa dalibai cewa an basu hutun kwana arba'in da biyu. Don haka ranar dakwana arba'in da biyi ta cika kowacce daliba kadata kara ko kwana daya. Idan ta kara to za.a koratagida. Baza a karbeta ba. Sannan tayi musu nasihohiakan idan suka je gida su dinga taya iyayensu aikibanda yawo a gari gidan kawaye balle kuma masu samari. Mataimakin principal ma ya tofa albarkacinbakinsa. Ya jawa daliban kunne akan su zamamasu da.a da ladabi da biyayya a duk inda suke.Saura malamai ma suka yi musu nasihohi akan suyiamfani da abunda principal ta fada musu damataimakinta. Sai kuma daga karshe malami uku da suka zo bautar kasa suka yiwa dalibanmakaranta sallama akan in sun tafi sun tafi kenanba zasu dawo ba. Malaman yan bautar kasar suneuncle haisa, rose iliya da hassan bawa. Dalibaimasamman ma yara sunji ba dadi saboda sun sabada malaman. Musamman haisam saboda kirkinsa da wasa da dariyarsa yasa kowacce daliba tahi tanasonsa. Musamman daliban da take koyarwa sunamatukar bakin ciki da rabuwa da malaminsuwanda ya kware wajen koyar musu da geography.Nanfa dalibai suka rode da surutu wasu na kukawasu na fadin'' we miss you ! We miss you so much!! Uncle haisam, we miss you more, stay don'tgo please. A haka dai principal da sauran malamaisuka fice suka umarci daliban suma su tafi dukwacce aka zo dauka. Hannah da nusaiba a bakinbarandar hall din wajen jakunkunansu suka zauna.Nusaiba tace'' allah yasa dady na tun jiya yaxo kano daga abuja. Ya kwana a kano yau da safennan ya kamo janyar kazaure. Kar ace yau zai tahodaga abuja gaskiya sai yamma zai karaso kazaurewallahi murna nake yi kaman za'a sani a aljannah.Dama ace ina rufe idona na ganni a gida'' hannahtayi murmushin karfin hali don babu walwala a zuciyarta dama ace duk wanda son zuwa gida yadaga hannu sai tafi kowa daga hannu dan ta zaunaa makaranta. Nusaiba ta kallo hannah wacce tunsafe bata murna. Musamman ma yanzu da taji ancehutun kwana arba'in da biyu za'ayi sai ranta yasake baci. Ga kuma babban tashin hankali haisam zai tafi. Nusaiba ta kula hannah ko irin dan dokintafiya gida bata yi. Sai surutu take ita kadai hannahbata sauraron ta sai wani tunani take daban.Nusaiba ta dan zungureta da gefen hanni tace''waike hannah meke damunki ko murna bakya yigida fa yau zamu'' hannah ta nisa sannan ta sake yin murmushin karfin hali tace'' me kika gani ?Wallahi nima ina murna dama na bude ido in gannia gida yanzu'' nusaiba tahi dadi da wannangudunmawar hira da hannah ta fara bata tace'' nikuma ina zuwa gida fruit salad zansa ayi min in ciwallahi shi nake marmari ''Nusaiba ta zabura tace'' meye makani,kwatantamin yadda yake nima idan naje gida incea soyamin'' hannah tace'' ai shi makani dafa shi akeyi. Ba kisan gwaza ba ? Nusaiba tace'' gwaza!gwaza!! Menene ma gwaza ? Oh cocoam zaki cemun. Kai allah ya sawake inci gwaza sai kace wata yar kauye ? Hannah tayi shiru don tasan ita yarkauye ce kuma acan su gwaza abun marmari ne.Nusaiba tace. A ina kuke samun gwaza ni banaganin ta ma ko a kasuwan abuja'' hannah tace mumuna samu'' uncle haisam ne ya tunkaro wajen dasuke zaune , su duka suka mimmike tsaye don girmamawa gami da cewa , good morning sir'' yace'' morning hannah, good morning nusaiba. Yauyammata sai gida naga nusaiba sai murna kike yiko ? Nusaiba tace yaya haisam murna yau nakelamar za'a sakani a aljanna. Haisam yayi dariya yace '' hannah kefa, kema kina murna kaman za a sakaki a aljannah ? Hannah tayi murmushin karfinhali tace'' eh'' ina murna nima, shigowar wata motakirar end of discussion ce ta katse hirar da suketazo ta tsaya. Kafin mutumin da yake ciki ya fitodaga motar nusaiba idris ta daka tsalle mike dagudu ta nufi wajen motar nan tana cewa babama oyoyo. Ya taho shima da saurinsa ya rungume ta suduka murna suke yi. Nusaiba ta ruko hannunmahaifinta ta nufo wajen da malam haisam dahannah suke zaune su duka suka mike dongirmamawa. Nusaiba tace, ga class master mu danake baku labarinsa a wasika nace shi yake kula damu uncle haisam sunansa. Alh idris yayi dariyayace. Oh uncle haisam duk wasikun nusaiba sai tarubuto mana labarinka da kai da kawayentahannah da rauda. Haisam yayi murmushi yace allahsarki ai ga kawarta hannah , hannah ta duka tagaishe shi ya mikawa haisam hannu suka gaisa. Nusaiba tace'' baba daga wannan hutun unclehaisam ba zai dawo ba. Alhaji idris ya ce da haisam''ai dama teaching practice kake yi ananmakarantar ? Haisam yace ''eh bautar kasa(N.Y.S.C)nayi kuma mun gama. Alhaji idris yace badadi yara sun saba da kai gashi zaka tafi, mun gode allah ya saka da alheri. Haisam ya ce '' ba komai aikannena ne.nusaiba ta ciro takarda daga jakarta dabiro ta mikawa haisam tace ya rubuta mata lambarwayar sa. Ya karba ya rubuta mata. Ta karba tamikawa hannah tace '' hannah rubuta min lambarwayar ki a kasan ta uncle haisam'' hannah tayi turus ita bata taba taba wayar bama balle ta sanyadda ake amfani da ita har ta san wata lamba.Haisam yayi sauri ya ce a'a ke rubuta mata taki zatakiraki. Nusaiba ta rubuta lambar wayarta ta mikawahannah, hannah ta karba. Daga karshe hannah takamawa nusaiba jakarta suka nufi wajen mota. Alhaji idris ya bude but haisam ya kama ya saka.Nusaiba ta rungume hannah su duka sunahawaye. Nusaiba tace'' kina zuwa gida ki kirani awaya kuma kullum zamu dinga waya munagaisawa. Alhaji idris ya dafa kansu ya ce '' ku dainakuka hutu za kuje yana karewa zaku dawo ai baku rabu ba gaba daya. Nusaiba da mahaifinta sukashiga mita ya ja suka tafi hannah da haisam sunadaga musu hannu har suka kure sannan sukakoma inda suke zaune da suka zauna. Sai gacincirindon dalibai suka zo suka zagaye haisamkowacce na baiyana rashin jin dadinta game da barin makarantar da zai yi, haisam ya baiyana musucewa in allah ya yarda duk term zai dinga zuwayana ganin su. A haka suka dai suka dinga wasada dariya kamar yadda suka saba rauda ma takaraso wajen ta zauna a hirar da ita basu lura dasanda motar gidan su ta shigo ba, sai kawai suka hango auwal wan rauda ya tinkaro su. Rauda tamike da gudu taje ta rungume yayanta, yanakarasowa ya mikawa haisam hannu suka kashe yace'' malam ,malam haka kake sa daliban naka agaba kuna rera hira ? Haisam yayi murmushi ya ce''bankwana muke yi kasan daga yau shikenan bazan dawo ba'' auwal ya ce wai har kun gamabautar kasar haisam yace ''kwarai kuwa ba famanake da kai ba kazo ka dinga yi mana dan kwanabiyu ma kaki to gashi nima allah yayi min komawagida gaba daya mun zama daya. Ya ce'' lallaishekara kwana ce kamar yaune muka kawoka kamar kayi kuka baka san kauye. Haisam yatuntsire da dariya ya ce'' gashi kuwa na saba yanzuhar bana jin dadi zamu rabu da dalibaina, nan daiauwal ya sami kujera ya zauna shima dake gwaninwasa da dariya ne da mutane ya dinga hira dadaliban nan yana zolayarsu dakyar haisam ya banbaro shi daga wajen daliban nan, auwal dazolaya ya sami yara yana ta zolayarsu musammanhannah, duk da ma baisan yadda take da haisamba yana tayi mata wasa wai ita balarabiya ce takoya masa yarensu yana tambayarta me ake cewayaro da larabci? Tayi dariya tace ban sani va shi a tunaninsa taki fada be kawai baisan ita babalarabiya ba ce. Auwal ya mike ya ce da daliban to ragowar kwakida kanzo na tafi tunda kun zama yan kwantai ba'azo daukar ku ba. Ya kallo hannah ya ce'' ke yaryemen jirgin kasarku baizo ba kema mun tafi munbarki sai kinfi kowa kwantai saboda ke ba yar kasaba ce. Hannah ta kyalkyale da dariya sauran dalibai suka ce'' mu bama cin kwaki bamu san ma yaddakanzo yake ba allahnya sawake kuma mumayanxun nan za'a zo daukar mu. Haka wasa dadariya aka dinga yi da auwal da su hannah haisamna gefe yana kallon yana dariya yace'' da hannahkema dauko jakarki kizo mu tafi na riga na muki signing ke da rauda mu tafi kawai. Auwal ya ce dahannah ''ah ke da nace sai kinfi kowa kwantai ashetare zamu tafi dake ko a filin jirgi zamu ajiyeki ne akano ? hannah tayi dariya tace ''oho ni dai banyikwantai ba'' haisam ya dauki jakar rayda cimaksaboda nauyi ba zata iya dauka va ya kai ya saka a mota.Auwal ya ce da hannah'' kawo kema in taya kitunda vaki da karfi don nasan a garinku bakwa cintuwo sai yar gurasa da zuma ko ? Hannah daimurna take kawai da ba gida za'a kaita ba kanozasu wuce da yaya haisam. Rauda da hannah sukaje suka shiga mota a gidan baya suka zauna, yaya haisam da auwal suma suka shiga motar yayahaisam ne yake yukawa auwal yana zaune a gefe,suka nufi get din fita. Dalibai na daga musu hannuhar suka tafi.rabon rauda da ta yiwa hannah magana tunjiya yau ko magana bata yi mata ba saboda tsabankishi da ita wai saboda yaya haisam yana ji da itaitama yace kanwarsa ce, yanzu taga yan uwantakarta tabbata gata a motarsu yaya haisam zai wuce daita gidansu ma. Ta kalli hannah ta yamutse fuska tace'' kema kano zamu dake kenan, daman a kanokike baki taba gaya mana garinku ba ! Hannah tayishiru ta rasa amsar da zata bata. Haisam ya ce ''ehrauda da ita zamu kano a gidanku ma zata zaunakinga sai ku dinga karatu tare ko ? Rauda tace'' saikace basu da da gida ai a gidansu a nemeta. Cikin rada hannah tace'' babu wanda zai nemeni, ni bazani gida ba. Ta mudubi haisam na kallonta yayimurmushi kawai. Haisam ya nufi cikin garinkazaure auwal ya dubi haisam yace a'a haisam inazamuje mu da zamu kama hanyar kano. Haisam yace'' cikin garin zani akwai wacce zamu dauko. Basu tsaya a ko ina ba sai kofar gidan uwar biyu damana shirye take suna aika yaro yayi sallama ya ce injimalam haisam sai ta fito da gyalanta daman a shiryetake tsaf ta fito. Bayan sun gaisa haisam yace da surauda su matsa mata ta zauna, suka matsa ta shigata zauna a kujera baya sannan suka gaisheta dukkaninsu. Haisam yaja mota suka tafi bai tsaya ako ina ba sai a babbar tashar kazaure ya tsaya yajuya ya kalli uwar biyu da hannah yace'' to ananzaku hau mota ko ? Uwar biyu tace'' eh akwai motahar babban mutum a nan'' uwar biyu ta yunkurazata fita ta juya ta kalli hannah wacce bata da niyyar fita bata ma san da ita za'a fita ba a tunaninta uwarbiyu ce kawai zata sauka ita kuma su kara gaba sutafi kano sai taji uwar biyu tace'' to hannatu fito mutafi ko ? Cikin rudani hannah ta juya ta kalli haisamdon jin abinda zaice sai ya rasa me zai ce matakawai ya sunkuyar da kansa kasa ya kasa magana, ya fito daga motar ya bude but ya dauko jakarhannah. Nan da nan kwandastocin mota suka zosuna cewa'' babura zaku ne. Ko daura ? Uwar biyu''motar babura zamu hau sai mu sauka a babbanmutum. Haisam ya mikawa kwandasata da zasubabbam mutum jakar hannah, uwar biyu tace '' af har yanxu hannah bata fito daga motar bane ?Haisam ya leka cikin motar ya tsaya yana kallonhannah baice mata komai ba, ta sunkuyar da kaicikin sanyi jiki ta jawo jakar litattafanta (schoolbag)ta rataya ta juyo ta kalli rauda ta kalli auwaltace'' na tafi sai anjimanku'' rauda tace au har dake zaku shiga motar haya kin fasa zuwa kanon ne ?Hannah ta gyada kai kawai sannan ta fito. Yayaauwal yana yi mata wasa yana cewa, af ashe yarkauye ce ma, motar babura zaku hau ko? Hannahta fita ba tare da ta bashi amsa ba,. Haisam dahannah suma suka nufi cikin tasha dama uwar biyu da kwandasatan daya dauki jakar sun shiga tasha.Motar bus ce wacce baifi mutane hudu ba ta cikaba. Uwar biyu ta zauna a kujerar baya aka sakajakar hannah a but hannah ma taje kusa da uwarbiyu ta zauna, jikinya sanyi kalau kamar marar lakahankalinta a tashe yake kamar wacce za'a kaita lahira ba gidansu ba. Haisam ya zaga ta wundon dauwar biyu ke zaune ya danko kudi ya mika mata yace' ga wannan kuyi kudin mota dan karku mastu kibiya kudin kujerun bayan a barku ku kadai sannanki fito ki shiga aishalle super market kafin mota tacika ki siyowa hannah sabulun wanka, wanki man shafawa dana gashi. Biskit da alewoyi ta yiwa yangidansu tsaraba.?ya sake deno wasu kudi masuyawa yace wannan kuma ki ajiye da zarar hutu yakare ya rage kwana biyu kije ki taho da ita kikawota gidanki zanzo in kara yi mata siyayya namayar da ita makaranta. A cikin kudin ki bawa mahaifinta dan na kashewa ki gaya masa lallai lallaihutun kwana arba'in da biyu aka basu da zararhutu yana karewa zaki zo ki dauke ta inji ni zakice.Ki san dai kalaman da zaki gaya masa na kwantarda hankali kada ya hanata dawowa kinsantsofaffin nan namu, kice ke uwar dakin tace a wajenki take a makaranta na hadaku, kice inagaisheshi da kyau. Uwar biyu tayi godaya tashialbarka kamar ita aka bawa kudin ko jikarta. Yadauko wasu kudin ya mikawa uwar biyu yace'' kisayawa hannah sarka da dan kunne na jiyal maikyau ki bata'' uwar biyu tace'' kai kudin ai yayi yawa malam haisam duk a cikin wannan ya isa nayimata siyayyar'' ya ce ''ba komai na gode uwar biyuallah ya kiyaye hanya'' tace amin malam mune dagodiya'' ya zagayo jikin wundon da hannah kezaune tayi tagumi ta langwabar da kai a jikinwundon mota jawaye ne yake sulalowa daga idanuwanta daya bayan daya. Haisam ya kalletayayin da yaji kamar zuciyarsa zata fashe dontsananin tausayinta , yayi karfin hali yace'' hannahkukan meye kike don kawai anyi hutu zaki tafigida ? Ai hutu na karewa uwar biyu zata je tadaukoki kinji ko ? Zan zo inyi miki siyayya na mayar dake makaranta, yanxu idan kika je gida kinakuka baba zaice wahala kike sha a makarantar yace ba zaki dawo ba. Amma ki nunawa babamakarantar da dadi ga ladabi da biyayyar da akekoya muku ga karatu da abinci a wadace shi kansazaice ki dawo, kinji ko ? Hannah ta gyada kai ta fara share hawayen idonta. Yace gaba da cewa'' kiyihakuri da abun da iya abu take yi miki hutu nakarewa uwar biyu zata zo ta daukeki ta kawo kimakaranta. Sannan kullum ki rika zuwamakarantar islamiyya kina kuma duba litattafankina makarantar boko don karki manta karatu kinji. Allah ya kiyaye hanya hannah. Ya juya ya tafi,muryarta yaji ta rushe da kuka, ya juyo ya tsaya cakyana kallonta sai ya rasa me ma zai ce mata sai yajuya ya tafi da sauri. Yana mai tsananin damuwa datakaici.kukan zuci kawai yake. Ba tare da ya cewa suauwal komai ba, ya ja mota ya fara tukawa. Canrauda ta nisa tace'' yaya haisam daman hannahfulanin daura ne, ko ba daura zasu ba ? Haisam yayidan murmushi kawai. Auwal yace'' haisam ka cikashige shige ina ka samu wannan buzuwar har da kakarta kuma? Haisam yacce'' wai shige shige ni dakai za'a san me shige shige naga daga zuwa harkasan su naja'at suleman ko banga sanda takebaka adiredhinta ba balle ni dana shekara amakarantar'' auwal yace to ya isa ga wannanzabiyar a baya ta bude kunnuwa tana daukar rahoto'' haka dai har suka isa kano jifa jifa haisamyake magana babu abunda yake tunawa sai halinda hannah zata kasance a gidansu. Zuciyarsa cikeda tausayinta kulle kullen yaya zaiyi yaci gaba dataimakonta yake gashi kuma ya bar makarantar,har suka isa kano . A nasarawa g.r,a suleman cresent gidan su haisam yake, suka shiga cikinkatafaren get din gidan . Bayan auwal da rauda sunshiga sun gaisa da hajiyar haisam sai suka yi mususallama suka nufi suma nasu gidan da yake lamidocresent basu da nisa sosai. Alhaji shitu mukhtar sunan mahaifinsu rauda,mahaifiyarsu kuma hajiya jamila sunanta alh. Shitumuktar haifafen garin kano ne, dan unguwankabara ne tare sukayi firamare da sakandire damahaifin haisam abokaine tun suna yara. Haj.Jamila kuwa mahaifiyar su rauda mutumiyar chadi ce ya aureta. Allah ya albarkacesu da 'ya'ya uku,yaya auwal shine wanda ya kammala karatunlikitansa a america yanzu cikakken likita ne. Sai antiramla wanda ta gama sakandirenta a wannanshekaran tana jiran sakamakon jarabawarta tawuce jami'a bayan an cancara bikinta da angonta haisam, saita fara karatu a gidanta, sai yar autarsurauda wacce yanxu take ajin farko a sakandire.Tsantsar yan boko ne yaya uku sun ishesurayuwar duniya suna basu cikakkiyar kulawa datsantsarso da kauna. Allaha yayi musu arziki maiyawa don haka a daula suke ta ko ina hutu, ba su fi shekara biyu da dawowa nijeriya ba kasancewaralh. Shitu muktar yana aiki a embassy, shinejakadan nigeria a america {ambassador} don hakaduk a can suka yi karatunsu har mahaifiyarsu haj.Jamila acan tayi digirinta.al'amarin hannah da uwar biyu kuwa, bayan tafiyar haisam uwar biyu tayi sauri ta sauka daga motartaje ta yiwa hannah siyayyar kamar yadda malamhaisam ya umarceta da tayi. Ta dawo cikin mota dasauri ta iske motar dai bata cikaba , bayan mota tacika suka kama hanyar tafiya. A hanya uwar biyu taci gaba da lallashin hannah tana bata baki dakyar tayi shiru da kukan da take yi. Ta dade daman tanaso taji labarin hannah da dangantakarta da malamhaisam, saboda tsananin kulawar data ga yana yimata, cikin wayo da dubara irin na manya uwarbiyu ta dinga bugun cikin hannah tana son tajilabarina. Abunka da yarinya kuma mai neman agaji da take yi ta ko ina hannah ta fayya cewa uwarbiyu komai daga biri har wutsiya. Uwar biyu tatausaya hannah ta sake jinjinawa malam haisambisa jihadin da yayi saboda allah na taimakonhannah. A garin babban mutum suka sauka aka saukemusu jakarsu . Tun daga sauka hannah ta farafaduwar gaba tazo garin da bawa ya fita jin dadi.Uwar biyu ta lura da hakan sai tayi ta bata baki tanakwantar mata da hankalinta. Kawayen hannahmaza da mata yan garin suka baibayeta suna kallonta wasu kuma suna shishshige mata harrububin yi mata magana su ke. Masu daukar matajaka suka dauka suka dunguma zuwa gidan suhannah. Samarin garin sai kallon hannah suke ganisuke kamar ba hannar da bace da suka sani. Tayijawur da ita tsaf tsaf. Babban mamakin kambas din da ta dana a kafarta suke kallo wasu na cewatakalmin yan ball tasa, wasu na cewa na faretinsojoji ne. Mamaki ya ishesu yadda akayi hannah tazama haka kamar baturiya a wata guda nan danan, kyau na zuba duka cikar garin da batsewarsababu mai kyawun hanne da gogewarta. Nanfa samari kowa ya hau cewa gaskiya tawace wannan.Wancan na cewa na rigaka. Kawayenta da yawasun kudiri niyyar suma sai sun tuburewa iyayensuan kaisu makarantar kwana irin ta hannah donsuma su goge suyi jawur haka. Kafin hanne takarasa gida labari ya kai cikin gidansu ance ga hanne nan zuwa ta zama fara kal kamar baturiya itada wata tsohuwa. Farin ciki ya rufe mahaifinta yaiwuf ya fito kofar gida ya tsaya yana murna yanajiran isowar hannensa(yar boko). Budar bakin iyaabu kuwa sai cewa tayi watakila ciki aka yi mata amakarantar tayi haske don hanne ba fara ba ce kal. Surutai dai na hassada da bakin ciki barkatai tadinga yi.Hanne na doso kofar gida ta hango mahaifintasai su duka murna ta lullubesu. Hannah ta karisa dasauri taje ta rungumeshi kamar yadda taga sunusaiba suna yima mahaifansu sai hawaye suke itada mahaifinta. Iya abu a tsakar gida ita da yayantababu wanda ya amsawa uwar biyu sallamarta da tayi, sai malam habu yace shigo kawai ai ba zasuamsa muki ba'' ya shiga daki ya dauko tabarma dasauri ya shimafida mata ta zauna a sanyaye cike damamaki irin wannan tsana da ake yiwa wannan yarkaramar yarinya wanda ma yake sonta an tsaneshi.Hannah taje gaban iya abu ta durkusa ta gaisheta ko ta amsa ta juya ta gaishe da yayyenta 'ya'yan iyaabu kenan suma suka kwata abunda mahaifiyarsutayi. uwar biyu ta rike baki tace ''oh ikon allah bayinallah me yayi zafi hannah nawa take ? Don allahkuyi mata yar fara'a mana ko taji dan sanyi yanzuko dokinta bakwa yi kusan wata biyu bata nan, aidarajar sabon idon ni bakuwa kwa raga mata harin tafi'' suka yo ca akan uwar biyu uwar biyu nayi yayan nayi, ta mike tsaye ta juya ta kalli hannahwacce ta kame a jikin katanga tana makyarkyatahawaye ne ke zuba daga idanuwanta tasan yauduka da zagi allah ne kadai yasan iyakarsa da zatasha. Hawaye ya kecewa uwar biyu tace'' hannah yihakuri wuya bata kisa ko anki ko anso gidan ubanki ne duk inda kika je sai kinzo gidan dole,''iya abu tace'' gidan uban nata ya gagareta zamaidan naso ba. Malam habu shima yayi jugum yakasa magana tashin hankali ya isheshi sabodayana tausayin hannah yasan wahala zasu ci gabada linka mata ganin allah ya rufa mata asiri tayi kyau, uwar biyu ta fita malam habu ya bita hannahma ta bisu da sauri, uwar biyu tasa gefen gyale tashare hawaye tace'' allah yana nan, malam ni yaraikece. Malam haisam malamin daya karbeta ahannunka din nan. Malam habu ya katseta yace ''ehna gane kiyi mana godiya da kyau da kyau na gode madalla. Tasa hannu a dan tofi ta dauko kudimai dan afki ta bawa malam habu'' inji malamhaisam ya ce a bashi nasa ne na kashin kansa banamakarantar hannah bane. Da zarar hutu ya kare itada kanta zata zo ta dauketa, malam habu yayi shiruyana sauraron uwar biyu sai girgiza kai yake kawai yana mamakin wannan tara ta arziki da haisamyake yi musu yana fadin ashe akwai masu halinsahabba a duniyar nan masu kyautar da dukiyarsuga mabukata irin malam haisam. Malam habu yadago ya kalli uwar biyu yace'' kema daya aikokikika rike amana allah ya saka miki da gidan aljannah dashi da yake mana hidima allah ya bashida mai yi masa haka munji dadi mun gode. Ni inanan wata rana na gaza barci ina tunanin ko yayayar baba, kome take ci a makarabntar na bartababu abinci? Ashe tana cam ta fini koshi, kalliyadda tayi bul bul ah alhamdulillah. Maigari ya aiko da garin kwaki kwano biyu da suga rabin kwanosai kudin motar zuwa kazaure ya ce in kai matamakaranta wallahi matar nan tawa data ga garinnan da kudin mota sai ta sulalo ina bacci ta sacekudin motar ta tilla ledar garin ya dinga tsiyayewa akasa, da naje na shaidawa mai gari ba kiga cin mutuncin da suka yimin ba wai daman talauci yaisheni na sami kayan gwamnati ina wadaka dashi,su babu ruwansu ya dai ya ta ce in barta yunwar takasheta. Nayi kuka da hawaye nazo na zauna nahakura sai addu'a na dinga aikamata daga na allahya hadata da mai bata. Allah ya amsa addu.ata gashi bamu girbe amfanin gona ba shine yasa kotaro nakan tashi babu a aljihuna. Uwar biyu tace,kaico haka kake rayuwa ta malam ? To ni daishawarar dazan baka dan allah dan annabi(S.A.W)duk runtsi duk wuya ka toshe kunnankakome za'ace game da karatun hannah karka cire ta daga makaranta. Babu sisinka. Ba kai zaka dauketaba. Bakai zaka mayar da ita va nice zan dingakawota ina zuwa ina daukarta sai dai ka bata izinikarka hanata saboda karatu ne kawai zai farfadoda hannah ta sami yancinta da jin dadin rayuwartaanan gaba, amma azabar tayi yawa. Malam habu ya ce da gudu kuwa zan barta, aini badan za'ace nasiyar da yata ba, ko ace na kaita birni tana iskancida ko hutu ma sai ince ta dinga yi a gidanki ammayanzu kowa yaji a rediyo an yiwa 'yan makarantahutu ba aga hannah ba za'a fara titsiyeni datambaya a fada. Uwar biyu tace allah ya kyauta ni zan koma, ga sabulai can a jakanta da mayukanshafawa malama haisam ce don allah a dinga bartatana wanka da wanki da kitso ba kamar yadda akakawota ba, kazan kazan ina amfanin kazanta ?Uwar biyu ta fara tafiya bayan sunyi sallama damalam habu yana ta godiya, hannah ta rushe da kuka ta bi uwar biyu da gudu ta rungumeta suduka kuka suke rusawa hannah tace''uwar biyu karki tafi ki barni wuya bake sha ni zanbiki gidanki in zauna a can. Daya daga cikin 'yayaniya abu musbahu shine ya fito daga cikin gidan aguje uwarsa ta turo shi yazo ya dauko mata hannah aka dake suna labe a zaure suna jin dukmaganganun da suke yi. Ya dauko ta aka ya mikata cikin gida ya rufo kofar zaure sai kukan hannahne yake tashi ya cika unguwar kai kace rai ake zaremata saboda irin karar kukan daga ji ba karaminbudu ake yi mata ba, malam habu nata kokarin bude kofar yana bugun kofar kamar zai balla yanaso yaje ya ceci 'yarsa uwar biyu ta juya ta tafi tanarusa kuka kamar ranta zai fita, tsananin bakin cikida tausayin hannah ne ya cika mata zuciya. Tana jinsamarin dake zazzaune akan benci suna jiyo kukanhannah suke cewa''to baiwar iya abu tazo har an fara nada mata dukar kai wannan yarinya allah daiya rayata kar itama wuya ta kasheta kamar uwarta.Haka hannah tayi ta zama cikin wahala da kuncida azabtarwan iya abu har hutun makaranta yakare. Ana saura kwana biyu a koma sai ga uwarbiyu tazo daukan hanne. Tunda iya abu ta ganka tahau fada ta inda take shiga ba ta nan take fita ba,anan ne malam habu yake fada mata , kinsan cewa tayi indai da ranta hanne ta daina karatu tundawata gulma aka hada na kaita gidan yan gayubabu wata makaranta. Wuf iya abu tayi tayo wajedaga cikin daki tazo ta tsaya a dokin kofa tanagirgiza ta kama kugu tana kallon uwar biyu ayatsune. Babu abunda uwar biyu take sai kallon wuyan iya abu galleliyar sarkar jiyal din da tasiyawa hanne ce a wuyanta. Muhajana 'yarta kuwariga da siket 'yar kanti ta hanne ce a jikinta, saigamusbahu shima yazo ya wuce da jakar hanne arataye a bayansa (school bag)wai daga kasuwayake. Iya abu tace'' bai gaya miki ba na hana karatun hanne ko bai fada miki ba ne ? Iwar biyutace '' shine mahaifinta shine kuma mai iko da'yarsa bake ba. Ni kuma akan kin barin yarinyarnan ta tafi zan iya cin dammara mu daku da kowakuma daga na har gaban mai gari zamu je dakeidan kika kwatanta hakan. Iya abu tayi shiru tasan idan aka kaita kara wajen maigari tasan bazai bibayanta ba kasancewar sun sha gogawa akan zatahana hanne karatu bata ci nasara va. Iya abu tanisa tace to kije dawan da kanki ki kirawo hanne'yata ba zata ba. Taja hannun 'yarta mahajana sukashige cikin gida.malam habu ya leka kofar gida ya kira musa dan makwabtansu ya ce yaje dawa yaceda hanne tazo yanzunnan ta koro kiwan su dawogida. Uwar biyu ta tabe baki gami dayin ajiyarzuciya tace'' rabon gado akayi da kayan hannetunda ranta ba'a jira ta mutu ba. Caraf iya abu ta fitoashe a labe take tace'' an raba kayan hannen ko hannen naga dama zan iya rabata balle kayanta.Duk gulmace gulmacen da kuke hadawa ya kare akanku babu wata makaranta da ake kai hanneyawon bariki kawai ake koyawa yarinya ta samoabin duniya'' uwar biyu tayi dariya shekeke tace''wannan yawon bariki na hanne don ke da yayanki take yi irin wannan bushasha da kayan yarinya. Dayake itama uwar biyu badaganan ba wajen iyamasifa da yaba magana suka yi tayi dakyar malamhabu ya hana uwar biyu magana ya ce ta yi shiru takyaleta, iya abu tayi fada tana shiga da fice bakinciki ya lullube mata zuciya kamar zata fashe ganin anzo za'a dauki hanne a tafi da ita wajen da takehutawa. hannah ta shigo a sanyaye tana fargaba tanatunanin me tayi kuma aka ce ta koro kiwo ta dawogida yanzu. Tana shigowa sai taga uwar biyu damahaifinta a zaure a zaune ta daka tsalle tarungume uwar biyu tana mai tsananin murna dafarin ciki tace. Iya daukata kika zo yi mu tafi'' uwar biyu tace'' yanzu kuwa shiga ki dauko kayanki mutafi. Hannah tayi kasake a tsaye murna ta koma cikitayi kamar zata fashe fa kuka. Uwar biyu ta kalletatace'' hannatu lafiya meya faru kuma kika zamahaka lokaci daya kamar mai shirin rushewa dakuka ? Uban yace da kika ce taje ta dauko kayanta shine jikinta yayi sanyi ai babu kayan duk sunkwashe. Harda litattafan makarantar sun yayyagasun siyarwa da mai kosai wasu'' uwar biyu takwada salati tana cewa'' harda manyan litattafankaratu masu tsada suka yayyaga mata ? Iya abutayi wuf ta fito tace da uwar biyu !! Ki kiyayeni don kin zake dawa, karfa ki kuskura ki cika min cikiba'aja dani an yayyaga littafin kyi abinda zakiyikuje ku saya mata wasu ta kawo na sakeyayyagawa muje duk inda zamu je aikin banza.Uwar biyu ta mike tsaye ta juya ta kalli malam habuwanda yayi tsuru abin duniya ya isheshi ya kasa magana tace '' malam na tafi da hanne allah yanabayan mai gaskiya kuma duk dan hakin da karaina shike tsone maka ido zakaran da allah yanufa da cara ko ana muzuru ana shaho sai yayi.Hanne mu tafi garin da ake kaunarki. ''iya abu tarako su har kofar gida tana zagi tasa hannu ta fallawa hanne duka a baya gami da angazata ta tafitaga taga zata fadi uwar biyu ta riketa tajahannunta suka tafi. Hanne ta rushe da kuka uwarbiyu fadi dake. Duk abinda zaki yiwa hannah bakiisa ki hanata numfashi a duniya ba tunda bake kikahalicceta ba'' suka kama hanya suka tafi, suna ji iya abu ta koma kan mahaifin hannah tana zazzagamasa masifa yayi shiru kamar bada shi take ba. A tasha uwar biyu ta siyawa hanna sabon silifasdomin na kafanta wari da wari ne, suna zaune amota uwar biyu take tambayar hanne abubuwanda ake yi mata. Hannah ta zaiyana mata tsaf tacekusan kullum sai an lakada mata duka an kwacekayan sawarta da jakunkunanta, sabulan ma da mayukan shafawa ko sau daya ba'a barta tayiwanka da suba. Tana dai barinta taje makarantarislamiyya kullum shima saboda tana tsoron maigarine. Hanne ta sake dagulewa kamar ba itace tayikyau din na ba das da ita gwanin sha'awa, yanzu tadawo furtutunta, yagulallun kaya uwar biyu tace'' yanzu har kayan makarantar taki(uniform)duksakawa suke ? Tace eh ta rarrabawa jikokintawasu, wasu kuwa ta sayarwa 'yan jagorar makafi.Bani da sauran kaya sai wannan na jikina, uwarbiyu ta nisa tace allah ya saka miki, kuma wannanyaro haisam shima an sake ja masa sabon aiki'' zugum suka yi su duka kowacce tana tunani harsuka isa tashr kazaure babu wacce ta sake yinmagana suna isa gida uwar biyu ta shirgowahanna abinci mai yawa da mamakinta hanna tatashi dashi tasha ruwa. Bayan sun huta uwar biyutasa 'yarta halima ta wanke mata cukurkudeden gashinta , hannah ta sallah wanka. Kafin magarubahar an gama rangadawa hannah kitso,Sai suka ji ana rangada sallama uwar biyu tacehanne ta leka zaure taga waye yake sallama . Tanalekawa sai taga safiyanu ne abokin yaya haisam,rike da wata katuwar jakar bacco babbar ta karshea girma. Hannah tayi dariya '' tace lala yaya safiyanusannu da zuwa . Ya ce yauwa har kinzo ,hutu ya kare ko ? Hannah tace'' eh ka shigo mana'' dakyaryake jan buhun a kasa saboda a shake yake damda kaya. Suka iske uwar biyu a tsakar gida. Lalemar haban, uwar biyu take cewa hannah tayi saurita shimfida tabarma ya zauna. Bayan sun gaisa da uwar biyu ya fara zazzagekayan dake cikin wannan katuwar jaka siyayyarhannah ce ta makaranta (provision) kaya ne abunbaya lissafuwa komai akwai kai kace kanti za,abude uwar biyu ta rike baki kawai tana kallon ikonallah, tace '' safiyanu wannan kaya ai ya yiwa hannah yawa. Safiyanu yayi murmushi ya ce aikudin da haisam ya bani ne masu yawa ne ya ceduk ayi mata siyayya a wadace. Nima da kainanaga ya dace na bar siyayyar nan haka ba donkudin sun kare ba . Uwar biyu tace ai gara da karago kudin don sai an sake siyan sababbin uniform da litattafai. Safiyanu ya ce ina nata nada , ko dukterm ake sake wa ? Uwar biyu ta gyara zama ta farabawa safiyanu labari duk abunda ya faru da kayanhannah tun daga biri har wutsiya. Safiyanu yatausayawa rayuwar hannah duk da yake damahaisam ya gaya masa kadab daga ciki. Ya nisa ya ce'' abun babba ne kudin da yawa musamman nasayan litattafan karatun(text book)masu tsada negashi haisam din bama ya kasar. Uwar biyu tacebaya kasar ina yaje ? Nifa tun ranan hutu ban sakesashi a idona ba. Safiyanu ya ce'' ai kuwa bai dadeda tafiya ba shi da mahaifiyarsa suka tafi london kinsan shirye shiryen bikinsa ake yi shi da yayansawatakila nan da wata uku za'ayi don haka damanzaiyi wuya haisam ya sake dawowa kazaure tundabautar kasa daman yazo kuma sun kare. Nima dayake daman a kano na sanshi a can muke haduwa.A can kuma ya ce zai dinga kawo min kudin siyayyar hanna. Yanzu dai abunda za'yi duk abindaya tashi na game da makarantar hannah a gayamin zanyi ko nawa ne zan ranta masa nasan zaibiya ni don haka daga yau zuwa gobe zanyi kokarina saisayo mata uniform din da takalmi da kumalitattafan. Zuwa gibe telan daya dinka mata wancan zai dinka mata da wuri . Jibi dai zasu komamakarantar kafinnan insha allahu komai yakammala. Uwar biyu tayi murna dajin bayanansafiyanu tayi ta godiya. Amma hanna ta fita yinmurna da farin ciki don ita da a tunaninta za'acekarshen karatunta yazo tunda yaya haisam baya nigeria to sai taji safiyanu ya ce zai ranta a dinkamata. Suka yi sallama da safiyanu su duka suna yimasa godiya ya tafi, akan jibi hannah ta kwana dashiri zai kawo mata kayan ya kuma mayar da itamakaranta. Haka kuwa aka yi hannah tana dayadaga cikin wadanda suka fara dawowa makaranta tun karfe sha biyun rana, kafin yamma makarantata cika makil kowacce ta dawo tana tsoro sabodaprincipal tace duk wacce ta kara kwana dayabaza'a karbeta ba. yaya haisam baya nan kishin da rauda take yi dahannah ya kau yanzu suna zaune lafiya wasa dadariya, sai dai su dukkansu basa jin dadinmakarantar sosao saboda babu yayansu. Haka dukyan ajin uncle haisam basa jin dadin sabon classmaster dinsu saboda baya tarairayarsu kamar haisam. Kowacce bata manta da nasihohin da unclehaisam yayi musu ba akan suyi karatu sucijarabawa idan ba haka ba za'ayi musu repeating .Kowacce ta dage da karatu ba dare ba rana donhaka j.s.s 1a is the best class in f.g.g.c kazaureyawanci a wajen assembly malamai suna fadar haka principal tasa a tafa musu, tana kuma alfaharida su tana yabawa tsohon class master dinsuhaisam saboda tasan shi ya gyara ajin haka. Tanakuma nunawa sauran malamai dasuyi koyi dashidon ire iren su haisam a makarantar.Bayandawowar daliban makaranta da kamar wata guda. Ranar wata litinin da safe ana assembly sai kuwaprincipal tayi musu albishir da cewa.kwararrenmalamin nan uncle haisam ya dawo makarantar amatsayin permanent teacher. Tasa wani malami yaleka waje ya shigo da haisam saboda a waje la labekada su ganshi suki tsayawa ayi assembly suyi taife ife don haka ya tsaya daga waje. Malam haisam na shigowa dalibai gaba dayansu yara da manyasuka hau ihu da tafi murna kuwa ba'a cewa komaimusamman a wajen hanna. Wai! Yau da za'a budezucoyar hannah aga irin farin cikin da yake cikinzuciyarta da abun da yawa. Dakyar dai dalibansuka dan tsagaita da ihu aka karasa assembly kowacce ta tafi ajinta. Yan ajin su rauda kuwa hadabaki suka yi suka yi kungiya suka nufi ofishinprincipal dauke da manya manyan takardu sunrubuta kamar haka '' we want our former classmaster uncle haisam back.'' waisu zanga zanganlumana suke yi principal da sauran malamai suka sha dariya sannan ta basu amsat cewa za'a dawoda haisam dinsu, su koma aji. Sannan suka tafi sunamurna. Haisam ya dawo yaci gaba da rike ragamarshugabancin ajinsa j.s.s. 1A. Hutu yana zuwa karshe jarabawa na karatowahaisam naci gaba da yiw dalibai nasiha dasu dageda karatu musamman ma hannah yana ci gaba danunnuna mata duk abunda bata gane ba. Ba laifihannah tana sake kokartawa fiye da waccan termdin. Ta fara gane ayyukan makarantar sosai tana kuma gane turanci tana yi kuma. Wannan termdinma kamar wancan sunyi jarabawa sun gamasannan malamai sun yi kokarin sun kammala fitarda sakamako. Haisam ya tara yan ajinsa ana gobehutu ya bawa kowacce sakamakon jarabawarta.Wannan ma kamar waccan bata sake zani ba rauda shitu muktar itace tazo ta farko. Nusaiba ta biyu,pamella matin benin ta uku. Hannah ce dai ta samici gaba maimakon tazo ta goma data zo wancankaron yanzu sai tazo na takwas.Hannah tayi murnahaisam har ya fita murna ganin ba kudin banzayake kashewa ba, da bata lokacinsa a banza ba. Kamar wancan hutun, ranar hutu principal ta yiwadalibai assembly, hutunne bashi da yawa sosaikwana ashirin da takwas ne kawai zasu yi a gida.Amma wannan karan direban gidansu rauda yazodaukar rauda sai haisam ya ce ta tafi shima dagagidansu za'a aiko da direbansa yazo ya daukeshi. Bayan tafiyar rauda babu dadewa sai ga dalleliyarmotar haisam kirar jeep da mahaifinsa ya bashibayan ya gama bautar kasa, muntari sunan direbanhaisam, yazo ya duka ya gaishe da haisam, haisamya nuna masa jakar hannah ya ce ya dauka ya sakaa but. Bayan ya saka hannah ta shiga baya, haisam na gaba direba mutari yana tukawa suka fita dagamakarantar. Haisam na nunawa mutari hanya hargidan uwar biyu kamar waccan lokacin suka iskeuwar biyu a shirye tsaf. Ta fito daga gida bayan sungaisa, haisam yace da uwar biyu su dauki jakarkayan su shifa cikin gida a ajiye, kaya kala biyu kawai za'a bawa hannah da silifas faya amma duksauran a ajiye da litattafanta. Da yake safiyanu yabashi labarin duk yadda uwat biyu ta gaya masaabunda ya faru da kayan hannah. mutari direba ne ya taya su da shiga da kayan cikingida. Uwar biyu ta zaba ma hannah kayan da zatasaka ta cire uniform da kambas aka bata silifas dawani kala daya a leda wanda zata tafi dashi. Bayansun fito daga gida sai suka shiga mota suka tafi,basu tsaya a ko'ina ba sai a tasha. Wannan karan ma har bakin mota haisam ya raka su hannah yadauki kudi mai yawa ya bawa uwar biyu yacr suyikudin mota na zuwa can tayin na dawowarta,sannan a ciki taba mahaifin hannah na kashewa taajiye wanda zata je ta daukota idan hutu ya kar e.Yayi wa hannah nasihohi ya bata hakuri game da halin da take ciki a gidansu.Daga karshe yayi musu fatan allah ya sauke sulafiya. Ya juya ya tafi uwar biyu na tayi masa godiyadashi masa albarka hannah na rusa kuka Zaharaddeen Shomar Whatsapp 08168575100 GANGARJIKINSA NA AURA 1 Part 3 Posted by ANaM Dorayi on 02:12 PM, 30-Apr-15 Under: Gangarjikinsa ta Aura Haka daiuwar biyu da hannah suka kasance idan hutu yarage yan kwanaki sai uwar biyu taje ta daukohannah. Haisam kuma baya gajiya da yi mata siyayya duk abunda za'a bukata na rayuwarmakaranta. Ko yayan masu hannu da shuni na makarantarbaza su nunawa hannah gata ba. Idan aka yi hutuhaisam yana kaisu tasha ya sasu a mota uwar biyuta kaita gida. Amma kuma kaya kadan uwar biyutake bawa hannah ta tafi dashi garinsu kadandinma bata dawo dasu,iya abu ta kwace tabawa yayanta ga bakar wahala da ake bata, wujigawujiga hannah take dawowa hutu kamar ba ita ba.Saboda wahalar da take sha tayi duk sai tayi duhu.Amma daga ta dawo makaranta kafin hutu ta sakefes da ita. Kwanci tashi wannan ne hutun dasu hannah in sundawo makarantar zasu shiga senior class wato s.s1. Don haka duk uniform dinsu sai an sake musuna seniors daban na junior class daban. Don hakatun kafin uwar biyu taje ta dauketa haisam yakawowa uwar biyu uniform din hannah ta ajiye har ya dinka mata ya canja mata school bag tsaleliyairin ta manyan dalibai, akwati maitaya biyu yasayamata babba da karama. Babbar ta zubaprovision karamar ta kayan sawarta, kamar yaddayaga yayan attajirai ana yi musu idan suka shigaajin manya. Ranar da aka dawo makaranta safiyanu ya dawo da hannah. A duk lokacindasafiyanu ya kawo ta makaranta takan kirawokawayenta su zo su gaisa, yayan ta take cewakamar yadda taga kowacce tana kiran kawayentata gaisa da 'yan gidansu. Duk 'yan makarantar sunayiwa hannah kallon wata 'yar gidan gawurtaccen attajiri ko nusaiba da rauda basu san ba dagagidansu ake yi mta siyayyar nan ba saboda haisamyayi mata gargadi kada tagayawa kowa labarintata rike surrinta. Rauda da nusaiba sun dauka uwarbiyu kakarta ce kuma babban mutum din da suketafiya duk hutu garin kakanninta take zuwa. Ko a hira hannah bata cika bada labarin yan gidansu basai dai tayi ta sauraron na mutane. Masassakin budurci ya fara sassaka hannah ma'anata zama budurwa kyau ya sake fitowa. A gaskiyakyan hannah bazai iya suffantuwa ba, farinta yasake haskawa, gashin kanta ya kara tsawo sabidatayi wayon gyarashi ga mayukan gashi kala kalada haisam yake siya mata. Ranar wata social night da daddare ne haisam ya hango hanna, nusaiba darauda sun sha wandunan jeans da teasirt sun nufikatafaran kantin siyar da kayayyaki kala kala dakecikin makarantar. Suna tsaye suna siyayya saidariya suke suna tafi, cikin sanda ya karasa kantindon yaga me suke siya haka suna dariya. Wai ashe rigar nono zasu fara sawa 'yan kanana. To shine yakawo musu guda dai dai suke jin kunyar siyakyma. Hannah tace'' ni dai ba don kunce a siyobireziyar na dani ba da bazan siya ba, yanzu fa dolebazan dinga sakewa ba zan dinga gani kamar anaganin shatinsa ko hannuna yana fitowa ta riga kowa yana gani'' rauda tace'' caf aini da ganganzan dinga sakin hannun rigata don ta fito'' nusaibabata ce komai ba ashe ta hango uncle haisam abayansu a tsaye tana ta kifta musu ido basu ganiba. hannah tace'' ko da yake mun zama senior har 'yanj.s.s 1 ma naga wasu suna sawa fa, nusaiba zabi.Hannah na daddagawa, nusaiba tayi gyaran muryataga dai basu san uncle haisam na bayansu ba. Saitace '' ba ruwana ga yaa haisam nan yana kinku''.Haisam ya kyalkyale da dariya. Sai su duka suka juyo nan fa hannah ta wurgar data hannunta taruga a guje, nusaiba da rauda kuwa suka cusa tasua riga suma suka arce. Haisam yazo ya dauki waccehannah ta wurgar shi da mai kanti suka dingadariya. Haisam yace su hannah yan mata Haisam ya dada kyau sosai hankalinsa ya kwantaya zama mai kudi baya ga albashinsa accountmahaifinsa ya bude masa yana zuba masa ribar dasuka ci a kamfaninsu duk wata yake warewa'ya'yansa, ga hannah ba laifi ta girma wahalar datake sha a gida ta ragu abubuwa da yawa ta fara takawa iya abu da 'ya'yanta burki tana kwatarkanta dole wasu abubuwan suke raga mata. Donhaka kallo daya zaka yiwa haisam kasan dan gidanwani gawurtaccen mai kudi ne saboda suffarsa ta'ya'yan hutu ce, fari ne sol fatarsa mai haske, yanada dara daran ido da dogon hanci, mai yawan gashin?idon dana gira gazar gazar . Wani dan siriringemu ne ya zagaye dan madaidaicin bakinsa(kautar million)gashi dogo mai dan madaidaiciyarkiba. Haisam yana daya daga cikin irin da kowacce'ya mace take mafarkin samun irinshi. Gashi amakarantar yan mata masu ji da kudi da kyau ga gayu. Don haka kusan kullum haisam sai ya samiwasikun 'yan mata akan teburinsa a ofis dinsa sunjefa masa. Wai suna sonsa soyayya mai tsananikuwa sai kawai yayi dariya ya yaga ya zubr kodakuma ya hadu dasu bazai nuna musu yagasakonsu ba. Yan aji shida ne suka fi yi masa wasikun amma wasu 'yan aji biyar din suna rubutomasa shi gani yake suk suna duk hauka suke zasugaji su daina. Gasu kyawawa dasu amma bayaganin kyawun, 'ya'yan attajirai amma shi baidameshiba, shi dai kawai yazo ya cika burin da yakudira ya tafi. senior juwairiyya itace shugaban dalibai (headgirl) juwairiyya kyakykyawan gaske ce fara solharma akan ce suna kama da hannah. Gatamahaifinta wani babban manager ne a wani bankia lagos tana ji da gata da dukiya ga tsananin kokaritafi kowa kokari a shekararsu. Amma sai allah ya jarrabeta da tsananin son uncle haisam tun ba yauba gashi da yawa daga cikin malaman sun mato a sontaita bata son su ta fi son haisam. Ta aika masa dawasiku sunfi a kirga amma shiru ko alama haisambaya nuna mata na yaga wasikarta . Da ta gaji daaika masa da wasikun saita dinga aika masakawayenta baro baro suke tarar sa su gaya masa amsar daya basu cewa yayi duk yarinyar data saketarar sa da maganan juwairiyya saiya sabar mata.Don haka juwairiyya ta rasa yadda zata yi ta shawokan wanda take so . Ranar litinin da daddare an fitodaga (prep) juwairiyya ta sami kan wata baranda tazauna tana tunani don ita son haisam har ya fara dasa mata wani ciwo da yake damunta a zuciya hartake kasa karatu sosai gashi kuwa tafi duk yanmakarantar kokari, don haka nema aka nada tashugabar dalibai. Zaman da tayi wucewar haisamkawai take son ta gani sannan ta iya bacci. Salahanura itace babbar aminiyar juwairiyya tazi giftawa zata tafi ajinsu taga kawarta a zaune a baranda itakadai, taje wajen ta dade a tsaye a kanta juwairiyyabata sani ba. Ta dafata sannan tayi firgigi ta dago .Salaha nura ta zauna a kusa da juwairiyya tace''juwairiyya tunanin meye kike, ke kadai kowa yanaaji ? Juwairiyya ta nisa tace allah salaha inasan uncle maikayu sosai har kamar zan zautu'' salaha tatuntsire da dariya tace'' uncle haisam wai? Shegusunan da kuka saka masa kuma, to juwairiyya yayazamuyi kin rubuta a rubuce yaki kin aikemu yazazzagemu ko ke kika je da kanki ba zai yadda ba.Kwarjini yake mun ba zan iya tarar saba'' inji juwairiyya salaha tace'' to meye abun yi? Juwairiyyata zunguri salaha ta nuna mata haisam ne yatunkaro inda suke daga staff qurters ya karasoinda suke su duka suka gaisheshi cikin ladabi. Yace ''oh shugabar dalibaice da labour prefect ? Sukace mune si'' yace ''wato kun kora yara aji ku kunzo kun zauna kuna hira ko? Kamata yayi kufi kowakaratu yanzu tunda kune masu shirin yin waec daneco da jamb ko? suka amsa eh ba hira muke bawani muke jira'' juwairiyya ta marairaice muryatace'' amma na ganshi yanzu zamu tafi damanfatana in ganshi kawai ''haisam ya gane abunda take nufi sai kawai yayi sauri ya katseta ya ce'' idanzaku tafi gashi kuje j.s.s. 1a science class ku bawahannah abubakar imam. Ya mika mata wata leda adaure ya juya ya nufi ofishinsa ya shiga sannan yarufo kofar. Juwairiyya tace da salaha''kinga abunda nakegudu ko shariya ce da wannan mutumin ko fuskabaya bani da zan gaya masa abunda yake damuna.Salaha nura tace'' to wai ni na lura meye yaketsakanin uncle haisam da hannah abubakar imamne ? Kamar duk makarantar nan yafi kulata komai hannah zaka ji yana ambata kamar shi ya radamata sunan. Juwairiyya tace'' ance abokin wantane wai, kuma saboda rauda shitu kawar hannah itaai kanwarsa ce. Salaha nura tace'' to kanwarabokinsa ai zai iya sonta. Salaha ta karbi ledar da yabawa juwairiyya ta kwance sai suka ga magunguna na ruwa da kwaya ne , na zazzabidana tari ya saya mata. Salaha ta tabe baki tace.Lallai magunguna ya sayo mata tafi karfin ma tashana clinic din makaranta kenan'' juwairiyya tace'' zomuje nasan abunda zan hadawa yarinyar na''salaha ta taso suna tafe suna zancen suka nufi ajin su hannah. Juwairiyya tace'' ba uncle haisam yacekada wata ta kuskura ta kara kai masa sakona bato ni kuma hannar da yake ji da ita daga yau ita zandinga aike wajensa. Salaha tace'' kwarai kuwahaka za'a yi muga ko itama zai korota din'' tawundo juwairiyya ta leka tace'' ina hannah abubakar ? Yan ajin suka ce'' gata can a sit dinta akwance bata da lafiya'' tace ''ko ciwon ajalo take tataso ta zagayo tazo ina kiranta'' nusaiba ce tatasheta tace '' hannah kije senior juwairiyya nakiranki'' hannah ta daga ido dakyar tace'' bazan iyatashi ba bani da lafiya'' jikinta zafi kyau kamar wuta. Jijiyoyinta kanta sunyi rudu rudu don ciwonda yake yi mata. Juwairiyya ta daka mata tsawatace da hannah ta taso allah yasa asibiti ne a kantaba jinya ba. Nusaiba da rauda suka rirrikota sukatasheta tsaye. Juwairiyya ta daka musu tsawa tacemusu munafukai su saketa tazo da kanta. Haka hannah ta fara tafiya tana rirrike bango ta fita tazagaya bayan aji inda suke. Juwairiyya ta mikamata ledar da haisam ya bayar a bata suka ce''gashi inji saurayinki. Hannah tayi jugum tanamamaki can tace waye'' waye kuma saurayina?Salaha tace'' zaki sashi munafuka. Juwairiyya ta mika mata wata takarda tace'' ki kaiwa unclehaisam kice ina jiran amsa yanzu kice nace mikikarki sake ki dawo min babu amsa'' hannah ta faratafiya jiri yana daukarta ji take kamar ta fadi sabodayini cur a kwance babu ko dan tea a cikinta. Ta isaofishinsa ta kwankwasa yayi mamaki da yaji ana kwankwasa masa kofa yanzu, ya tashi ya bude saiga hannah a tsaye. Mamaki ya kamashi yace''hannah lafiya ? Keda baki da lafiya kika iyatahowa? Hannah ta cije baki gami da rike bangokamar zata fadi tace'' aikoni wajenka aka yi'' yace''aike kuma, waye ya aikoki? Ta mika masa wasika tace ''inji senior juwairiyya da senior salaha suncedole in taho musu da amsa kar inzo babu amsa yabata rai ya karbi wasikar ya bude ya karanta.Wasika ce irin ta kullum daga juwairiyya ya cecirayuwarta tana sonsa.Haisam ya cikuikuye ya wurgar ya ce'' sun bakimagungunanki'' tace''ah ina ji sune anan'' ya karbaya bubbude yana tsiyaya mata a murfi yana mikamata sai ta karba tasha. Sai da ya tabbatar ta shadukka sannan ya daure ledar ya mika mata ya ce tawuce daki ta kwanta gibe idan taga baza ta iya fitowa aji ba tayi kwanciyarta zai sanarwa da dutymaster. Daga karshe ya ce'' sai da safe allah ya bakilafiya hannah. Tace amin '' har ta juya zata tafi sai tatuna ta juyo tace masa'' me zan cewa seniorjuwairiyya ? Ya ce'' kice nace tazo ta karbi amsar dakanta. Hannah ta amsa da to sannan ta tafi. Daman su juwairiyya na zaune a wata baranda suna hangosu. Hannah tazo wucewa suka kirata tace musu takai masa ya ce amsar taje da kanta ta karba. Salahatace'' jeki to'' juwairiyya ta nisa tace'' kinga haisamko wallahi wulakanci yake shirin yimin tunda ya ceinje da kaina ni nasan ba wata maganar amincewa zaiyi min ba. Saboda ai nagani cukuikuye wasikartawa yayi ya yar a kasa, ya buge da bata magani aidole ma son hannah yake'' salaha tace'' ammakuwa sunan yarinyar na gawa don sai taci ubanta amakarantar nan , mu 'yan s.s.3 muce muna sonsayaki ya so junior mu ai bazai yuba. Jeki kiji abinda zai fada muki don muci uwarta da hujja'' juwairiyyata mike ta nufi ofishin haisam tana wani karkaderiga tana gyara fuska. Tayi sallama gami da turakofar zata shiga ya dakatar da ita da hannu yace''tsaya daga nan baranda kiji abunda zan fada miki.Don me kika sake yimin aiken wasika bayan nace kada wanda ya sake zomin da wasikarki. Kumawanne rashin tausayi ne da zaki taso yarinya mararlafiya ki aikota, duk daliban makarantar nan, saihannah ? Me yasa sai ita zaki aiko juwairiyya ?Juwairiyya ta tsuke fuska tace'' amma uncle haisamduk aiken dana keyi baka taba kirawoni kace meya sa nake aiko kawayena ba sai dai kacewayan aiken duk wacce ta sake zuwa zaka sabarmata. Meya sa baka fadawa yar aiken ba a wannankaron sai ni ka kira ? Haisam ya fusata ya dakamata tsawa yace'' ina tambayarki kina tambayata ?To kar kiji yauce rana ta karshe da zaki yimin haka. Ki rike darajarki da mutuncinki a matsayinki na yamace budurwa. Idan sai kinyi soyayya a makarantaba karatu ya kawo kiba to ga sauran malaman dasuke rubibin sonki amma ni bani da ra'ayinsoyayya, this is the last warninng bana son na sakeganin sako daga wajen ki sai anjima kije. Wani jiri jiri juwairiyya take ji ta juya ta tafi tana kwafa.Salaha tazo ta tare ta a hanya tana cewa'' meyenake hangoki a baranda ofishinsa ma ya hanakishiga ? Juwairiyya tace'' ke dai muje in baki labarinyadda muka yi'' daman lokacin tashi daga prepyayi duka dalibai sun dungumo daga ajijuwansu sun doshi dakunansu. Don haka juwairiyya dasalaha nura sai suka nufi hostel a hanya ta zaiyanamata duk yadda suka yi da uncle mai kyau watohaisam. washegari talata da sassafe bakwai da rabia lokacin dalibai suke firfitowa daga dakunansuzuwa ajijuwansu domin daukar darussa. Uncle haisam a tsaye yake kem a bakin get din hostelyana kallon masu fitowa daga ciki, mamaki yakama dalibai ganin sabon al'amari meye unclehaisam yazo ya tsaya anan da sassafe haka bashine da duty ba, ba ranar inspection ba kuma.Kowacce idan ta ganshi sai ta duka ta mika gaisuwa ta wuce'' good morning sir'' can ya hangorauda da nusaiba da pamella suna tahowa daganesa ya dauka hannah ce sai da suka karaso yagababu hannah a cikinsu. Bayan sun gaisheshi ya ce''yau kuma ina hannah ko jikin ne ? Rauda ta waigagaba da baya taga babu kowa sai ta matso kusa dashi tace'' hannah ba lafiya tana clinic a kwanceacan ta kwana'' gabansa ya yanke ya fadi ya ce''zazzabin ne ya rufeta ? Nusaiba tace'' wannan yafizazzabi yaya'' rauda tace'' su senior juwairiyya nesuka yi mata duka da tsakar dare kusan dukkan s.s3 sai da kowacce ta doki hannah jiya ina ji a sume ta fadi da kyar matron suka zo suka hana su. Mumabamu san me tayi musu ba. Kuka mu ma mukakwana muna nan da nan haisam ya canja ido yakada yayi jawur gashin jikinsa ya mimmike kai kacemuku mukun sanyi ake amma duk da sanyin safiyazufa yake yi. . Ba tare daya ce tak ba ya juya ya nufi clinic inda hannah take a kwance ya same ta rikkicifbata sanma inda hayyacinta yake ba. Abinka dafarar fata sai sabun bulalan suka mata jawur a jiki ,har wuyanta da fuskarta shatin bulala ne lambar.Ya dade a tsaye yana kallonta kawai yasa hannu yacire mata wani ganyen maina daya makale mata a wuya a sanadiyar duka sai yaji jikinta zafi kaukamar wuta, yaja mayafin dake kan gadon yalullubeta. Babu kowa a clinic din nurse din ma batanan. Ya juya ya fita a fusace ya nufi ofishin principal.Ya shiga ofishin gami da yin sallama ya sami wajeya zauna bayan sun gaisa ta dubi haisam tace''haisam lafiya yau na ganka ranka a bace dukwannan fara'ar taka ? Ya ce''dole raina ya bacisaboda kusan kashe wata yarinya akayi a daren jiya a makarantar nan 'yan aji shida ne suka dakiwata yar aji hudu da tsakar dare kamar zasukasheta tana clinic a kwance'' principal ta zaburatace'' subhanallah'' ta danna kararrawa masinja yashigo tace maza yaje aji shida ya kira matajuwairiyya. Haisam da principal na zaune sunyi jugun kowa yana tunani a zuciyarsa. Can saigajuwairiyya ta karaso ita da wani malami mai sunasahabi tazo ta dutkusa a kasa ta gaishe daprincipal. Principal ko amsawa bata yiba ta rufejuwairiyya da fada tana cewa'' in har ba zaki iyahana a aikata laifi ba a makarantata banga amfaninki ba a matsayinki na shugabar dalibai''haisam yace'' madam ai itace ta gaiyato sauran yanaji shidan suka hadu sukayi dukan'' principal tace''oh har da ke head girl kuka hadu aka kusa kasheyarinya, kiyi kneel down yau sai kun yabawa ayazakinta'' uncle sahabi yayi carab ya ce'' madam tsaya kiji, juwairiyya ta fadamun duk abunda yafaru daman zamu taho wajenki muka hadu damasinja a hanya a gaskiya yarinyar ce bata dakunya wai cewa tayi zata yi dambe da head girlshine juwairiyya ta danyi mata bulala uku labourprefecr tayi mata biyu. Ga yarinyar can ma a aji tana daukar darasi babu wani zancen kisa'' haisam yafusata yayi kan sahabi da fada yana cewa'' karyazanyi musu? Yarinyar da duk makarantar nan babumai shirunta da ladabi yaushe zata ce zatayi fada dahead girl ? Kawai baza ka tsaya kayi bincike ba donsun gaya maka karya da gaskiya shine zaka yarda, kaje clinic kaga jikinta a farfashe bata san ma indahaiyacinta yake ba . Sahabi ya ce '' madam donallah ki raba mana rigima ki aika clinic a dubo idanakwai wata marar lafiya. Babu kowa ta warke tamike ba'a gabanmu hannah tazo ta wuce ba dazuko ba hannah ba ce wacce kake cewa an kusa kasheta ? Kuma kai duk wannan hakilon da kakecewa akan hannah saboda kai saurayinta ne fa shiyasa kake wannan sauran da ake duka ka tabamagana ? Principal ta lura maganar babba ce saimanya sai tace da juwairiyya ta tashi ta tafi zata aikoayi kiranta. Fuskar juwairiyya cike da murmushi ta fice principal ta kalli haisam tace'' kwarai tun ba yauba ansha fada mun kana soyayya da hannah.Dokar makarantar nan an hana daliba da malamiyin soyayya . Yanxu na gane manufarka don andaki budurwarka shi yasa kayi magana ko? Dagayau zan sa c.i.d kada ka kuskura in sake jin ance kana soyayya'' haisam ya fusata, ransa ya bacizuciyarsa ta hau tafarfasa. Ya dakawa sahabi tsawayaje har gabansa yana nuna shi da hannu ya ce''kai sahabi karya kake yi ni nafi karfin ka yi minsharri kai da juwairiyya zaku gane kuranku amakarabtar nan. Ni kake cewa ina son hannah ko ? Bayan da bakinka kazo ka sameni kana rokona inhadaka da kanwata hannah kana sonta naki nacekabarta tayi karatu ashe kana kullace dani kasaaka yi mata wannan dukkan ko ? Ke kumaprincipak kin goyi bayansu sun daki yar mutabe abanza ko ? To ni sai na daukarwa hannah fansa da kaina'' ya kada kai ya fice. Sahabi ya juya ya kalliprincipal yace'' kinji kuma inda ya lauya maganako ?tace ''kyaleshi bayan kai ma mr.ojo ya fadamun cewa son hannah yake don haka kaci gabada kula dasu. Haisam ya nufi staff qurters ya shigagidansa ya zauna a falon yana huci kamar ya kashe kansa yake ji saboda tsananin bakin ciki yau kodarasi ba zai je yayi ba. Yini yayi cur a gida ya kudiriniyyar zai dauki fansa akan duk mai hannu a cikinwannan al'amari , wai sahabi ne zaiyi masa hakasahabin da ke zuwa har gida yace ya taimakeshi yashawo masa kan hannah wai juwairiyya da kanta take cewa rashin kunya hanna tayi mata zata yidambe da ita wai shine tayi mata bulala uku itakuma principal da kanta take bin bayansu bayantasan hannah tasan halinta tasha yin kwatance daita a wajen assembly akan tafi kowa da'a da ladabishine har ta yarda da kintsin da suka yi mata ko da kyau, haka haisam ta dinga nanatawa a zuciyarsa .Haisam ya dinga nanatawa a zuciyarsa. Haisam baifita daga gida ba sai da yamma misalin karfe biyarya shigo cikin makaranta a lokacin dalibai sunaprep din yamma ya wuce kai tsaye ajinsa don yagajikin hannah, a zaune ya ganta a kan kujerarta ba laifi jikin burdin bulalan ya dan warware zazzabinya sauka sai dai bata iya bude idanuwanta sosai. Yace da ita'' hannah ya jikinki ? Cikin sanyin muryatace'' da sauki'' yace kinsha magungunan naki?Tace eh nasha'' wani masinja ya leko ajin yacemalam haisam kazo inji principal. A fusace haisam yace meye kuma? Dan aiken ya ce'' waya aka bugomaka zaka dauka a ofishinta'' ya ce gani nan zuwahaisam ya juyo ya dubi rauda da nusaiba ya ce'' kudinga kula da hannah ku tabbatar tana cin abincikunji ko ? Suka amsa da'' to zamu kula da ita.Sannan ya fita daga ajin ya nufi ofishin principal yana isa ofishin yayi sallama ya shiga ya gaisheta amurtike. Tace'' yayanka ne habibu yake son yayimagana dakai nace ya kira nan da minti biyar za.akira....'' kafin ta rufe bakinta wayar ta fara karahaisam yasa hannu ya dauka ya gaishe fa yayahabibu yaji da kyar habibu yake amsa wa rai a bace habib yace kai haisam mu fa ba yara bane kananakana ji ko? Saboda me zaka dinga yi mana wasa dahankaki ? Kace shekara uku zakayi a makarantarnan sannan ka bari yanxu shekara uku sun cika,Saboda me zaka dinga yi mana wasa dahankali ? Kace shekara uku zakayi a makarantarnan sannan ka baru yanzu shekara uku sun cika,last week da kazo aka gaya maka cewar ka barteaching dinnan ka dawo gida da kamfanoninbaba aiki yayi mana yawa muna neman ma'aikata, kace da zarar ka koma kafin karshen watannanzaka dawo gida kabar koyarwa gashi munji kashiru. Kujerarka na nan na jiranka ga ramla nan najiranka itama. Har anyi bikina da jidda har ta haihu'yar mutane na zaman jiranka kazo ayi bikinku. Waishin me ka zamar da mune, har nawa kake da zaka dinga juya mu ? Don haka karka sake nazomakarantar nan da kaina ka rubuta takardar barinaiki kabar koyarwa nan ka dawo gida muna nanmuna jiranka. Kai baka kishin dukiyar ubanka saigwamnati zata baka da kake mata wannan wahala,me kake nema ka samu wanda a gidanku baza a baka ba ? Haisam ya fusata yace'' ka gamamaganarka ? To bari in fada maka gaskiya ba zanbar koyarwa ba ina nan bazan dawo gidan ba'' yakifa kan wayar ya fice. Principal ta bishi da kallo harya fice. Wayar ce ta sake yin kara tasa hannu tadauka taji habib ya ce''ina haisam din? Tace ''ya fice'' ranki ya dade kema harda laifinki tun rannanbaba ya kiraki har gida ya ce kiyi murda murda kisaa koreshi daga makarantarki zai biya ki ko nawane. Kika ce bazai yu ba. Wannan yaron ko kasheshiza ayi bazai bar makarantar nan ba. Wanne irinlallashine ba'ayi masa a gida ba yaki ya bar koyarwa'' principal ta nisa tace'' habib tunda kajinace bazan iya sawa a kori haisam ba to babuyadda zanyi saboda wannan makarantar tagwamnatin taraiya ce daga kololuwa aka daukihaisam haka kuma korarsa sai daga can abuja.Dana bincika ma babban director na federal shine ya dauke shi aiki alh.sabi'u auwal abokinbabankune ko? To babu kuwa yadda za'ayi nahada baki dashi a koro haisam daga makarantarnan habib ya ce''zanzo makarantar watakila nan dasati biyu, idan na dawo daga tafiya dole ne ma yabar makarantar donyaga ana yi masa sakwa sakwa ya dauka tsoronsa ake yi don ni banga uwar dayake samu ba a makarantar'' a haka suka yisallama suka ajiye kan wayoyin. BAYAN SATI asheda sahabi ba kadai akwai malamai da yawa dasuke son hannah. Sai yanzu suka dinga baiyana.Ranar talata data zagayo haisam da sauran malamai uncle sahabi da uncle yusuf suna zaune a gindinbishiya da prep din yamma sai uncle yusuf ya aikawata yarinya ya ce taje s.s. 1a ta kira masa hannahabubakar . Haisam na zaune yana tunanin lafiyayake kiran hannah. Hannah ta karaso tazo tasurkusa ta gaishe su uncle yusuf bai amsa ba yace'' hannah yau zan nuna miki karshen taurin kai,girman kai daji da kai. Don haka kije ki karyo bulalakatuwa mai kauri dai dai tsawanki ki kawo min''haisam na zaune yana kallonsu hannah ta tashijikinta a sanyaye ta nufi dawa, can ba dadewa tataho dauke da wata zabgegiyar bulala. Tazo ta durkusa ta mikawa incle yusuf ya ce tayi kneeldown ta daga hannu ya kuwa tashi ya farazabgawa hannah wannan reshen. Haisam ya kauda kai gefe kawai yayi shiru, yusuf yayi mata bulalakamar sau takwas sannan yace ''kin san me kika yimin? Cikin sheshshekar kuka hanne tace'' ban sani ba '' ya sake daddagewa ya sakar mata wanidukkan yace'' kin tuna yanxu? Cikin gigicewahannah tace na tuna''ya ce'' to me kika min? Tacejiya daka aiko kace inzo in sameka a lambu banzoba'' ya ce'' yauwa ashe dai kin gane yau sai nalahira ya fiki jin dadi don kin samu ma ana sonki , ke din me da zaki yi min wulakanci? Sahabi ya tashiya karbi reshen nan ya zazzabga mata sau biyar dakarfi kuwa ya ce'' tashi saura ki ki zuwa nan gabaidan muka aika kiranki prep'' tana tafe tana rusakuka ta nufi ajinsu. Sahabi yana cewa '' bari mugazata zo da prep din daren kuwa? Idan bata zo ba wallahi doble din wannan zamu yi mata. Haisamyayi tsaki ya mike ya nufi ajinsu hannah. Zuciyarsacike da tsananin bakin ciki da tausayin hannah.Yaje ajin ya tambaya aka ce hannah bata shigo ba.Nan da nan hankalinsa ya sake tashi yayi waje dasauri yana dube duben ko daji ta tafi ta zauna tana kuka, yazo wucewa ta ajijuwan yan aji shida yajinishi kamar wata tana tsallen kwado ya leka tawundo da sauri yaga ashe a s.s.3a sun taru kusandukkaninsu suna azabtar da hannah ta jike dagumi sharkab saboda gwale gwale da duka.Juwairiyya ce rike da dorina a hannunta tana biye da hannah tana tsallen kwado tana fyauda mata. Afusace haisam ya daka musu tsawa duk sukawaigo wasu suka ruga ajijuwansu suka zazzauna.Ya hango wani masinja ya kirashi yace yaje daji yakaryo masa manya manyan reshen bishiyar mainaya kawo masa. Ya zagaya cikin ajijuwa ya ce dukkaninsu su firfito waje bai rage kowa ba duks.s.3 din, sun dauka abin wasa ne suna tafe sunarangwada suna tauna cingam, juwairiya kenansuka firfito waje daga ajijuwan ya ce'' su fara tsallenkwado suma, yaje cikin ajin ya tarar hannahsharkab tayi gumi ga sawun bulala nan duk jikinta lambar. Yasa hannu ya tasheta tsaye yace ta daureta tafi daki ta kwanta. Tana tafe tana layi tana rikebango ta nufi hostel.suna tsallen kwadon a duk yadda suka gadama a zatonsu zaice su koma aji su zauna sai sukahango masinja dauke da himilin bulalai kai kacejakuna za'a daka tafka tafka dasu. A fusace haisamya karbi bulala suna tsallen kwadon yana binsu dulwacce ta fadi kota tsaya a baya yana tafka mata wani dogon waje ya nuna ya ce har can zasu kaikuma sai su huyo. Haka suka dinga yi suje su juyohar sai da ya tabbatar kowacce ta jigata hawayenma ya kasa fitowa sannan ya ce su biyo layikowacce ta kwanta flate sannan ya shashsharbamata reshen nan sau gima sha biyu. Bayan jikinsu yayi kaca kaca ya farfashe kuka wiwi dankwalayensu a hannu ga kafa ta sage babu damartafiya. Juwairiyya tafi kowa shan wuya duka yayimata kamar allah ya ne ya aiko shi ko kirgawa mabaya yi daa bulalai suka karkarye yasa kafa yadinga ball da ita daman yana ciki da ita. Kuka wiwi suke suna bashi hakuri daga yau baza su sake ba.Sannan haisam ya gyalesu anan a kwance wasu adurkushe. Tunda haisam yazo makarantar nan baitaba zagin wata ba balle duka yau sai ga haisam yacanja fuskarsa babu digon rahama murtik da itakamar zai kashesu haka yayi musu ligi ligi dukkan da babu malamin daya taba irinsa a makarantar kodispline master baya yin irin wannan dukan. Labariya kai gidan principal , agigice ta fito ta taho a bakinofishinta ta gamu da haisam. Ta dube shi sai taga yacanja gaba daya sai taji ta shiga tsoronsa tayi masamagana. Can tace''haisam wannw irin duka kayiwa s.s.3 yau me suka yi maka haka? Ya juyo a fusaceya ce''ki tambayi kanki da kanki daman n fadarannan tunda baza ki iya daukar mayaki ba akanabunda su juwairiyya suka yiwa hannah to ni nadau fansa , kuma zan iya tin haka akan kowa dukwanda yake marmarin takurawa hannah a makarantar na'' principal ta rike baki kawai tanakallon haisam , ya wuce ya barta anan tsaye ya nufigidansa. Yana jiyo malaman da suke zazzaune awajen suna cewa'' ai kuwa yarinyar nan sai zamanmakarantar nan ya gagareta don sai mun zane ta,itama'' nan dai principal ta hau fadace fadace tana cewa'' dole ne na kira meeting da manyan yanfederal akan abun da haisam yake yi min amakaranta. magaruba tayi uncle yusuf da uncle sahabi sukanufo gidajensu ta jikin gidan haisam suka zowucewa yana jin abunda suke fada wai da prep dindare zasu kira hannah suyi mata dukan tsiya .Shima haisam sin yaji in da dadi. A haka suka rabukowanne ya nufi gidansa. Haisam na idar da sallar magariba yayi shigar wata yar riga mai gajerenhannu damammiya(body hook) ya dora wata suitaka ya fita ya nufi gidan sahabi. Ya kwankwasakofa, sahabi yazo ya bude fuskar haisam ce ya ganimurtik ta bashi tsoro. Yaja da baya da sauri. Haisamyasa hannu biyu da karfi ya angaza shi ya tafi taga taga ya fada kan kujerar dake falon. Haisam yashigo cikin falon ya mayar da kofa ya datse. Sahabiyayi tsuru tsuru a zaune haisam ya karaso indayake zaune yasa kafarsa daya ya taka kujerar dasahabi ke zaune ya duko dai dai fuskar sahabisuna kallon kallo . Sahabi ya yatsune fuska ya ce''meye haka haisam lafiya ko ka zama dan taadda ne kazo har gidana ka angajeni'' ya yunkurazai tashi taji haisam ya turashi karshen kujerawannan karon hannu yasa ya danki wuyan sahabi.Sai ido kuru kuru an shakeshi kai kace mujiya ce tafada rami. Haisam yasa hannu a aljihu ya ciro wata karamar wuka ta bude ta tana walkiya tasansanawa sahabi a hancinsa ya ce '' ka kula daabun fa nake so na fada maka idan ka kiyaye kakubuta idan kuwa kaki to kaiconka kaga wannanwukan zan iya lumata a cikinka ko na yanka ta awuyanka ka fadi ka mutu ko? To ina da niyyar aikata haka in har ka kuskura ka sakw takurawahannah a makarantar nan. Zan iya kashe ko wayeba kai kadai ba don haka ka kiyaye. Sannanhaisam ya sake shi ya mayar da wukarsa aljihu yajuya ya bude kofa ya fita yabar sahabi nan zauneyana tunani kamar a mafarki yau yaji kanshin mutuwa baro baro yana fadin''lallai haisam dagaske yake zai iya kis a kan yarinyar nan fa'' abayyane. haisam na fita gidan uncle yusuf ya shigakasancewat duk yawancin malaman samari nebabu mata a gidan. Daya taba kofar yaji a bude saikawai yasa kai. Kicibus suka yi yusuf ya fito dagawanka daure da dan tawul a jikinsa. Yayi mamakidaya ga haisam a tsakiyar falonsa ko sallama bai ji ba, murtik haisam yake babu walwala. Shima sai jiyayi an tunkudeshi kan kujera yayi masa gargadi,kamar yadda ya yiwa sahabi ya firo ya barshi nanzaune yana mamaki. Saboda tsabagen tsorata suyusuf ko fitowa basu sake yi ba sai da safe . Balle suje su daki hannah da daddare kamar yadda suka shirya yi, haisam ma tunda ya ya shiga gida baisake fitowa ba ba sai kashe gari da misalin shadaya na rana yana da lesson a s.s.2b zai yi musugeography yana doso ofishin principal ya hangomotar yaya habib yana cikin ofishin principal ,kuma yasan yau za'a yi tane ta kawai donshi babu mai rabashi da makarantar nan. Ya karaso da sauriya nufi ofishin principal tun daga kan baranda yakejiyo kukan hannah ya shiga a fusace gami fa yayelabulen kofar bazar ya tarar da hanna a durkushega jakar kayanta nan a gabanta, principal tanarubuta mata takardar kora {dismisal letter} takardar kora daga makarantar kwata kwata ga yaya habiba zaune yana cewa''ai idan yaga tabar makarantarzai bari shima dole ''a gigice haisam ya karaso yakalli yaya habib ya kalli principal yaga da gaskesuke sun sha kunu.Haisam ya wawuro wata adda a bayan kyaurenofishin irinta yankan ciyawa ya dora akan kirjinyaya habib. Wanda mamaki ya hana yaya habib yinmotsi daga kan kujerar da yake zaine, haisamyace''hakika zan iya kashe duk wanda yake dakokarin jefa hannah a cikin tashin hankali da wahala a rayuwarta. Ban dauka zan sameka kanadaya daga cikin irin wadannan mutane ba, ammaduk da haka ba zan karya alkawarina ba. Kaiyayana ne uwa daya uba daya da irin soyayyar damahaifanmu suke yi mana, ka duba kuma irinsoyayyar da muke yiwa junanmu don haka bana son na zama ajalinka . Ba kuma zan bar makarantarnan ba har sai na cika burina dana kudira akanhannah''hannun haisam rike da adda akan kirjinyaya habib karkarwa duk jikinsa yake hawaye neyake shatatowa daga idonsa haisam gaba ki dayansa ya canja, yaya habib ya tabbata haisam ya kai kololuwar bacin rai don shi yasan yadda bacin ranhaisam yake abun babu kyau. Da wuya dai yayifushi abu da yawa bai cika bacin rai ba sai an kaishi bango idan ya hau to kowa sai ya tsorata kumamai lallashinsa ya sauko sai an sha wuya kumaidan ransa ya baci zai iya yin duk abunda ya ce zaiyi. Hanna ta kwala kara tace'' yaya haisam kadaka kashe dan uwanka a kaina na yarda ni zan barmakarantar dan allah yaya haisam, dan allah kayihakuri''wani zazzafan hawaye ne yaci gaba dazubowa daga idanuwan haisam a tsaye yake kawaiya kurawa yaya habib ido rike da wannan adda a wuyan yaya habib. Principal kuwa tuni ta dagatsalle tayi lungu tana jiran taga yadda haisam zaiyida yaa habib sannan ya dawo kanta. A fusace yayahabib ya yinkura zai tashi haisam yasa hannu yaturashi kan kujerar ya koma ya zauna. Haisam ya ce''bani takardar hannunka''yaya habib yace son hannah kake? Ya sake fada cikin tsawa yace''tambayarka nake sonta kake shi yasa ka kasabarin makarantar? Haisam yace''burina ingahannah tana cikin farin ciki a rayuwarta kuma inkwatar mata 'yancinta kamar kowacce yarinyatunda ita ba baiwa bace gatan hannah allah, sai kuma ni a duk duniyar nan. cikin sanyin jiki habib ya mikawa haisam takardar asanyaye sannan haisam ya dauke addar daga kankirjinsa ya wurga bayan kyaure ya dauki jakarkayan hannah ya ja hannunta suka fice. Habib daprincipal suka bisu da kallo suna fita principal tayiajiyar zuciya don da kyar numfashinta yake fita saboda tsabar ta tsorata ta tabbatar yadda haisamya harzuka yau zai iya kashe yayansa balle kymaita. Bayan wani lokaci mai tsawo suna zaune shirubabu wanda ya iya magana suna tunani kawai,yaya habib ya nisa ya kalli principal ya ce'' madamyaron nan da gaske yake don jaka kada a kaishi bango ya zo ya kashe wani a dinga kai kawo akotu, ina ganin a kyalesu kawai don allah a dainadukan yarinyar balle har ya harzuka yayi kisadomin haisam zai iya aikata hakan tunda ya furtayana da zuciya sosai amma fa sai an kaishi bangodan bai taba zai yi kisa ba sai yau akan yarinyar nan, zanje in sanarwa da mahaifanmu'' ya mike yafita, principal kuwa da kyar take iya maganasaboda tsoron haisa tana ganin zai iya binta gidacikin dare ya kasheta. Daga karshe ta yankewakanta shawara gara taje ta sami haisam ta bashihakuri suyi sulhu . Ta kuma yi masa alkawarin baza ta sake yadda kowa ya takurawa hannah ba. Hakakuwa tayi ta sami haisam har gida cikin lumanasuka zauna ta bashi hakuri suka yi sulhu. Tana fitahaisam ya tuntsire da dariya dadi ya lullubeshoi yace HAISAM HANNAH!! Kwanci tashi su hannah sun shiga aji shida {s.s.3}sune manya . Cikin ikon allah da hukuncin allahhannah tazo tafi kusan duk yan makarantar kokarisaboda tun tana zuwa ta takwas ta fara zuwa tabiyar daga nan ta kwacewa pamella matin positiondinta ya zamana rauda ta daya. Nusaiba ta biyu ita take zuwa ta uku. Tafi tafiya saiga hannah tazo tadaya a ajinsu wani lokaci rauda ta kwace kayantaidan nusaiba mata hargistso sai ta kwance itama,haka dai ake ra fafatawa amma yanzu da sukashiga aji shida har malamai ma fada suke hannahtafi su rauda kokartawa don sau da yawa ko tambaya aka yi a aji hannah ce take amsawa sautari. Sannan a class work da assignment tafi kowa ci. An basu mukamai daban daban. Hannahabubakar imam itace shugabar dalibai {head girl}nusaiba mataimakiyarta. Rauda kuwa dake tayikaurin suna a wajen iya rawa da wasanni {games} harma ake mata lakabi da janet jacson sai aka batasocial prefrct da games prefect mukami biyu akahada mata kuma tayi murna da wannan mukaminnata. Duk ranar social night har koyawa yara rawardisco kala kala take yi. Hannah ma ta dace damukamin saboda ana son head girl ta zama mai kokari, wacce ta iya turanci sosai, mai gaskiya,ladabi da biyayya, mai kamun kanta ba ballagazaba, mai aji , da tausayi da kuma adalci to dukwadannan hannah ta hada sun don haka nema daaka tace aka zabeta. Domin a yanzu hannah kohausa bata cika yiba turanci ya kama bakinta sosai haisam har mamakinta yake idan yaji tana zubaturanci. Tana da jan aji hannah ba kasafai ta fiyeshiga cikin yan mate dinta ba suna hayaniya. Gatada tausayi musamman ga yara 'yan kananan aji.Babu ruwanta da cin zali kyma bata yardakawayenta suci zalin yara a gabanta. Tunda itace shugabar dalibai tana da ikon hana sauran prefect . wannan halaye na hannah ya sake fito mata dakyakykyawar surarta hannah ta sake gogewaabun har musaltuwa ta yi kyau kai kace ba yarafrica bace . Yaya haisam yasan irin mayukan dakayan sawar da suka dace da jikin hannah.Haisam yasan irin mayukan da kayan sawar dasuka dace da jikin hnnah . Tsadaddun riga dawando da sket kala kala yaya haisam yake hadawahannah sai dai kawai idan ta dawo hutu ta tarar yaaje mata a gidan uwar biyu, daman tun ba yaubabaya ga mahaifinta babu wani da take ganin girmansa a duniya irin haisam. Amma da yakehaisam mai wasa da dariya ne da dalibai suna wasada dariyarsu a aji kamar yadda ya saba yi musu tuna aji daya. A garin su hannah kuwa hannah hargixo take yi musu. Gani suke kawai baturiya tazotace itace hannah, duk ranar da hannah zata dawo gida hutu samari har tsayawa suke a hanyar dazata wuce suna kallonta mata kuma ta katangasuke lekowa. Ana cewa hannah ce fa yar malamhabu a garin turawa take karatu. Hannah sai tayimurmushi kawai ta wuce. A gidan su kuwa iya abuda yayanta daina magana suka yiwa hannah sunga ci gaba na hannah daga allah yake babu irin asirinda basu yi mata ba dan a korota daga makarantarko kuma ma ta haukace amma baici ba. Hannahtana dawowa da duk kayayyakin amfani wadandazata yi amfani dashi har hutu ya kare, ko ta bawasu iya abu da yayanta sai suce basa so. Sai tayi hutunta kakaf ta bar gidan iya abu bata bataabincin da suke dafawa ba. Ita kuwa hannahdaman tafi sin haka domin ita yanxu ta saba da cinmai maiko a makaranta tuwon dawa miyar kukasai su iya abu. Madara da biskit ne abincinta , alufge a jakarta a dakinta. Sabulan wanki dana wanka masu kamshi take amfani daus ita damahaifinta. Ta bashi yayi wanka ta wanke masakayansa. Malam habu yana jin dadi sosai dawannan abu da hannah take yi masa. Yasan doleidan hannah ta zo zata kawo masa kudi da abunduniya. Ga dinkuna da take kawo masa tace inji yaya haisam. Silifas dan madina dana gayu yanzumalam habu yake sawa. Tsaf tsaf dashi na kashewaya daina gagararsa. hannah ta zama tamkar wata tauraruwa mai haskea cikin taurari a makarantarsy. Akwai kungiyoyi{club} a makarantar da yawa, tun hannah tana ajidaya ta shiga kungiyoyi daban daban. Kuma dukwasannin kwaikwayo da za a yi a kowaccekungiya sai an saka hannah ko tana so ko bata so saboda kyawunta. Tun ana sata a matsayin yarinyahar aka zo ake saka ta a matsayin budurwa. Donhaka hannah ta kware sosai wajen iya wasankwaikwayo suna fita suje makarantu daban dabana fadin kasarnan, kamar su f.g.g.c azare,f.g.g.cbauchi, f.g.g.c. Kano,f,g,g,c, bakori da dai sauransu. Saboda kyawun hannah da iya acting dinta yajawowa.f.g.g. C kazaure suna da farin jini a wajendaliban sauran makarantu. Kowa ya budi baki saiyace kai a f.g.g.c. Kazaure da suka zomakarantarmu akwai wata mai kyau hannahabubakar ta iya wasa. A yau da yamma su hannah ne suke gwaji{rahazal}din wani wasan kwaikwayoda zasu he unity gwaram suyi sati mai zuwa.Kungiyar yan hausa fulani ne suke yi, malamhaisam shine shugaban 'yan hausa club, shinemalamin kungiyar{club master}don kawai yafarfado da al'adun hausawa a makarantar, ya kuma hada kan musulmai yara da manya ya zamana sunhadu a waje daya yare daya sunyi raye raye fawake wake da wasannin kwaikwayo tare. Hannah abubakar itace a mastayin yarinya maisuna talatu cikin wasan kwaikwayo, maryam tijjaniitace a matsayin saurayin ciki mai suna abdul.Haisam ne ya rubuta labarin wasan kwaikwayon. Ayadda wasan kwaikwayon yake maryam tijjani{abdul}saurayin ciki shine ai yi tafiya kasar libiya karatu sai yayi shekaru hudu acan sannan zaidawo. Ga budurwarsa hannah wato talatu a cikinwasan sunyi alkawarin zasu yi aure daman saitafiya ta taso masa yazo zai tafi ya barta. Damanhaisam ya gutsuro takarda ya rubutawa kowacceabinda zata ce a wahen sai ta rike tana karantowa harta rike da ka, kafin ranar da zasu yi ba sai datakarda ba. A yau kusan yan aji shida kakaf sunazaune a hall din nan wajen da ake gwaji{rahazal}din nan da wasu da yawa daga cikin yan aji biyar,hudu da uku yan kungiyar. Maryam tijjani {abdul}itace ta taho da jakar kaya katuwa a rataye a kafadarta tazo wucewa suka hadu da hannah{talatu} dauke da kwarya a kanta zata je kogi deboruwa. Abdul ya sakarwa talatu wani lallausanmurmushi na so da kauna cikin sassanyar muryahannah(talatu) tace''abdul ba dai tafiya ba'' ya ce''tafiya zanyi talatu nazo ne daman inyi miki sallama'' sai kawai kwaryar dake kan talatu ta fado kasa dangigicewa. Ta rushe da kuka. Abdul ya gigice yaajiye jakar dake hannunsa, hannah ta fara karantotakardar da haisam ya rubuta musu tace'' abdulkayi min alkawari ba zaka yi aure ba a cam har saika dawo ka aureni karka je can ka sami yar larabawa ka aura ni ka manta dani'' haisam yasatafi sai duk aka dau tafi a hall din. Haisam yacekunyi kokari wajen yayi kyau kema maryam tijjaniki dage ki bata amsa dan allah banda dariyar nanda kika saba'' maryam tijjani tace to bazan yi dariyaba'' ta daga ido ta kalli hannah(talatu) wani kallom soyayya da hannah take, tayi wani narai narai daidanuwanta kai sai kace a gaban saurayinta nagaske take. Sai dariya ta kwacewa maryam tijjanisai kowa yasa dariya. Haisam yace ''maryamgaskiya kina bata mana lokaci kullum muka zodariya kawai kike yi saura kwana uku fa mu fita excusion idan kinsan ba zaki iya ba nasawata''maryam tace''uncle allah hannah ce take sanidariya baka ga kallon fa take yimin bafa kamar tasami saurayinta da gaske sai kashe idotake''haisam yayi dariya yace''tsabar tafiki iyaacting kenan. Shi daman wasan kwaikwayo ana son duk abunda aka baka kayi kokari ka nunakamar da gaske ne. wajen kuka kayi kuka, wajen murnakayi murna . Kema kiyi mata kallo kamar kecesaurayin kin hadu da budurwar da kika fi so a duniya. Wannan yana nuna kenan hannah ta iyaacting sosai kamar da gaske. Kowa ya hau dariyaana yiwa maryam tsiya ''kema ki yi mata kallonsoyayyar mana ko baki iya bane? Haisam ya tashi yaje ya karbi takardar hannunmaryam ya ce''koma gefe ki dinga kallon yaddazamu yi sosai don ki koya'' ya ce da hannah''tokara karanto naki''babu kunya hannah ta narkarda idanuwanta ta kashe murya lallausa ta dubihaisam kallo ido cikin ido''abdul kayi min alkawarin ba zaka yi aure ba a can har sai ka dawo ka aurenikar kaje can ka sami yar larabawa ka aura ni kamanta dani anan'' haisam ma ya narairaice ido yakurawa hannah ido kawai wannan kallo da haisamyake yiwa hannah ya sosa mata wani waje axuciyarta, ya ce''talatu ba zan yi aure ba, kuma ba zan manta dake ba. Ko a ina nake, ko da gangarjikina bata tare dake ruhina yana tare da ke.,soyayya baiwa ce, hannah kina raina a kodayaushe . Ina sonki hanna'' taji gabanta ya fadi donjin yaune rana ta farko da hannah tasan ma'anarwakar nan da take yi tayi shiru tana tunani tana kallon yaya haisam ta san tabbas wannan wajen acikin wakar nan da take yi masa ya dauko kamardaga sama taji yaya haisam ya ci gaba da cewa''inasonki ina sonki hannah! Ba zan manta dake bakina raina har abada'' wannan karon bakarantowa ya ke a takarda ba kuma ba talati yace ba, hannah sai ta fara ja da baya taba tafiya ahankali tasa hannu ta rufe idanuwanta tanamurmushi. Kunya ta ka mata gaba daya yan kallonsun zubo mata ido suna kallon sarautar allah, domin kowa ya san wannan kallon kadai da sukeyiwa junan su yafi karfin gwaji balle kalaman da yake fita daga bakin haisam ba a jikin takardaryake ba. Sai yaja wani dogon numfashi ya juya yakalli sauran dalibai yace'' kuje ma karasa gwajin dadaddare'' ya fita ya nufi gidansa. Dalibai su ka firfitosuna gulmammaki'' wannan anya hannah da unclehaisam ba soyayya suke yi ba, ke kinga kallon da suke yiwa junansu uncle haisam kamar yarungumeta fa. Haka suka shiga dakunansukowacce ta nufi bangaranta. Rauda ta sami hannah a kwance akan gadonta tadora filo a kanta babu abinda take tunanowa saiidanuwan yaya haisam sai kuma tsananin mamakinyadda ya rike baitukan wakar nan da take yi masatun tana aji daya. Tace a ranta ashe ma'anar wakarkenan banda yarinta nake kai kaicewa nake rera masa ko da gangar jikina bata tare dakai ruhinayana tare da kai. Har nusaiba take cewa hannahmeye ruhi nace ina jin larabcine ashe ni ban sanhausa ba ce tsaba a lokacin . Ruhina , ruhina'' tsakitaji anyi a kanta ta bude ido sai taga raudaamurtuke. Tayi furgigit ta tashi zaune tace'' rauda har kun dawo? Rauda ta kaste ta tace''haka zaki cemana har mun dawo da acan zamu kwana? Komuma son maso wani muke yi da zamu bishigidansa? Yaya haisam dai yana da wacce yake sokuma an gama magana gara kowacce ta komakauyenta ta sami wani bakauyen ta aura amma haisam sai ramla. Hannah tace'' rauda me ya faru ,wani abun akayi ? Nusaiba tace'' ke rauda meyehaka wasan kwaikwayo ne fa kowa yasan gwajine ba gaske bane. Wai ke rauda me yasa bakya sona zauna lafiya ne ? Rauda tayi tsaki ta fice tana cewa'' duk gulmace gulmacen da ake ina sane. Dan iskan kauye yafi na burni iya iskanci da rashinmutunci ai. Hannah ta fashe da kuka, tayi kuka kamar ranta zaifita. Nusaiba na lallashinta da kyar hanna tayi shirusuka je suka yi alwalar magaruba. Bayan sallarisha'i sunci abinci karfe takwas dai dai sai suka jesuka kora dalibai kowacce ta fita ajinsu don yinprep din dare, uncle haisam ya fito daga gidansa takwas da rabi yazo ya kirawo yan hausa club donsuzo su karasa gwajin wasan kwaikwayon da sukeyi. Ta bayan wundo ya hango rauda tsaye akanbencin hannah tana ta gurza mata rashin mutuncihar cewa take da ba'asam asalin balbela ba sai tacemadina ne garinsu. Yaga hanna zaune tayi shiru tana hawaye, ran nusaiba ya baci ta taso tashigarwa hannah kamar zasu daku da rauda. Saihaisam ya leko ta wundo yayi musu tsawa ya ce sufito waje yana son ganinsu. suna zuwa gabansa kallo daya suka yi masa sukasan babu wasa yau a murtike yake kasancewarsunsan bacin ransa babu kyau sai kowacce ta fararawar jiki. Ya daka tsawa yace kowacce tayi kneeldown bayan sun yi ne ya tambayi nusaiba me yafaru. Nusaiba ta zaiyana masa dukkan abunda ya faru tsakanin rauda da hannah tun daga yammahar na yanzu ya juya ya kallo rauda yace'' raudahakane ? Ta gyada kai gami da tabe baki tace''haka ne kuma gaskiya na fada'' haisam ya fusataya kaiwa rauda mari tayi sauri ta kwanta a kasa baisameta ba. Tace' yaya haisam yau ni zaka mara akan hannah? Haisa yayi shiru hannayensa a cikinaljihu kansa a sunkuye a kasa. Can ya dago yace danusaiba ta tashi ta shiga aji. Ya dubi rauda wacce kedurkushe a kan gwiwarta a gabansa rauda tarushe da kuka. Haisam yace'' rauda tun ba yau ba,tun kuna aji daya na lura kin kafawa hanna karan zuka a makarantar nan. Yanzu kece kadai kikarage a cikin masu takurawa hanna zan iya daukankowanne irin mataki a kanki muddin baki fitaharkar hannah ba ki kiyae, idan kuma kin ki ni zanfiki farin ciki don zaki ga abunda zan zartar a kanki.Ko amratu 'yar shekara bakwai zan iya.hukuntata muddin ta nemi takurawa hannawannan alkawari nayi wa allah kuma sai na cika shidon hanna amana ce a wajena'' kamar a mafarkirauda take jin kalaman yaya haisam, tana fada aranta lallai abun nasa babbane da gaske yake'' daga karshe ya ce ta shiga aji tana sharbar kuka tamike a fusace ta shiga aji. Ya shigo shima ajin yakalli hannah wacce ido yayi mata jawur don kukayace hanna ki kira sauran yan hausa club ku tahohall ku sameni mu karasa rahazal din. Cikin ladabihannah ta amsa masa. Ya fita ya nufi hall. Hannah cewa'' rauda muje hall yaya haisam na kira'' tadago ta harari hannah tace'' bazan je ba kuma nafita daga club din ko za'a sani dole ne? Hanna zatace wani abu nusaiba taja hannunta tace ''kyaletamu tafi mu kira sauran. Hutu ya kusa karewa har ana shirye shiryen farafirst term examination. Kowacce karatu takehaikan, sunyi jarabawa an basu sakamako kafinranar hutu. Hannah ce tazo ta daya a ajinsuwannan karon, rauda ta biyu nusaiba ta uku ranarhutu bayan anyi assembly hutu da wur wuri kafin kowa ya fara tafiya haisam yazo ya sami hanna,rauda nusaiba da wasu kawayensu a zazzaune akan barandar hall suna ta hira. Bayan sun gaisheda shi sai ya ce'' hannah taso ga safiyanu yazodaukarki, idan muka saukeki a gidan uwar biyuzamu wuce dashi dan musa can jahar katsina acan yake neman aure zamu kai kayan gaisuwarsurukai'' su duka suka kyalkyale da dariya. Hannahtace ''oh yaya safiyanu daman aure zai yi ko ya fadamana sunanta ranar nida nusaiba muka ga hotontaa motarsa muka ce budurwarsa ce ya ce wai shi babudurwarsa bace'' nusaiba tace'' haka ne kuwa a bayan hoton an rubuta dan musa har nake cewadan musa kuma sunan mace dan musa ya ce ehhaka sunanta. haisam yayi dariya , sannan ya juya ya kallo raudatasha kunu ta kawar da kai gefe daman tundaakayi wannan abun bata cika yiwa hannahmagana musamman idan taga haisam da hannah.Ga uwa uba hannah ta kwace mata position tazo tadaya , sai take jin haushin kamar ta kashe hannah. Haisam ya ce'' rauda ni ba kano zanje ba sai mundawo daga danmusa don gida ma nace kada aturomun da mota auwal zaizo daukarki ko direba?Tace '' sai dai direba yaya auwal yanamaiduguri''yace''oh haka ne fa, to ki gaishe dasuhajiya sai wahen jibi zanzo kanon. Idan muka tafi yau ba damar muyi tafiyar dare dole mu kwanasannan washe gari mu dawo kazaure wata kila inkwana a cikin gari jibi muje kanon da safiyanu .Rauda tace zasu ji . Allah ya kiyaye hanya. Hannahta kira wasu juniors suka dauki jakunkunanta sukazuba mata a mota. Tayi wa kawayenta sallama tana zolayarsu su tana cewa yau itace farkon tafiya dukmakarantarn ta barsu su yan kwantai ne. Rauda tatabe baki tace'' yanxu wata kila har kowa ya isagida ke baki isa gida ba, saboda hanyar garinkukwalta ce sambel ba kasa ba'' hannah da nusaibane kawai suka gane rauda bakar magana ta fada, wato hannah bakauyiya cekenan take nufi saihannah tayi murmushi kawai ta tafi ta shiga motatana dagawa nusaiba hannu har suka fita get . a gidan uwar biyu su haisam suka sauke hanna ,haisam ya shiga cikin gidan bayan ya bawa uwarbiyu kudaden motarsu da wanda zasu kaiwamahaifin hannah suka yi godiya yayi musu sallamaya juya ta tafi har yaje kofar fita ya juyo yace '' koyanzu zaku tafi mu ajiyeku a tashe'' hannah tayi sauri tace yaya haisam da yamma zamu tafi ina soinje gidajen kawayena a nan cikin gari. Yayimurmushi ya ce'' wato akuyar daure ta samu sake,su hannah an iya yawo ko? Su duka suka yi dariyasannan ya fita. Damisalin karfe biyar uwar biyu dahannah suka isa babban mutum , suka je suka iske gida a hargitse anyi tashin hankali. Malam habumahaifin hannah kuka wiwi. Cikin rikice da rudanihannah ta tambaya meya faru babanta yake kuka.Iya abu ta tuntsire da dariya tayi buda da shewatace'' tambayi ubanki. Karshen tuka tiki tik yauallah ya nuna mana gaskiya'' hankalin hannah da uwar biyu ya sake tashi sosai, suna so suji me iyaabu take nufi da wannan habaici nata. Malam habuya sharbe hawaye da babbar riga ya ce''muje zaurein fada muku abunda ya faru'' da yake damantsakar gida suka iske su. Suka je zaure sukazazzauna malamhabu ya nisa gami da langabar dakai yace'' idan ka haifa dole a jawo maka, damanance dan kuka shi ke jawa uwarsa zagi. Uwar biyu dahannah su dai sun kagu suji abunda ke faruwayace'' yanzun nan babu dadewa watakila kunhadu da wata bakar katuwar mota a hanyar shigowa garin nan wata fitsararriyar yarinya cetazo ta cimun mutunci a kofar gidan nan har ta taramun mutane. Hannah tace''wacece baba? Cikinrudani da fargaba ta tanbaya. Ya ce'' farko da tazosai ta tsaya ta karemun kallo a wulakance sannantace naji kunya wallahi yasa naji kunya. Dama yarinyar yar talakawa ce yake bata mun lokaciakanta to baba bari in fada maka ka jawa yarkahanna kunne ta kiyayi mijina idan ba haka ba nizan zamo ajalinta domin zan iya kashe duk yarinyarda zata rabani da haisam abun sona. Kuma ka cireyarka daga makarantar nan domin idan bata bar makarantar va haisam ba zai bar makarantar ba yarabu da ita. Muddin hanna ta sake komawamakarantar to kuwa har makarantar zan bita inzartar da abun da na yi niyya. Ba tana takama itakyakykyawa bace to zan kwara mata wani abuafuskarta {acid}fuskar ta sale ta kwakwkwabe har makarantar zan tarar da ita in yaso sai inga fuskarda zai sota. Don soyayya hannah take yi da mijinava karatu ba. Har sakamakon jarabawar kanwatayake dauka ya bata tazo ta daya a ajinsu. To na gajiwannan shine lokaci na karshe dana bawa hannahidan taki ji ta koma makarantar to wallahi ta kuka da kanta'' malam habu ya sharbe hawaye yaci gabada cewa'' da wata kanwarta yar makaranta tanasanye da kayan makaranta irin naki yar baba itamatana taya ta suka yimin tas, iya abu na ihu tanadariya tana cewa daman ta sani ba tun yau bahanne karuwanci aka kaita tayi ba makaranta ba yanzu gari duk ya dauka maganar ake yi don agaban mutane aka yi haka. Tace hannah taci sa'ada bam sameta ba da sai ta faffalla miki mari sannansuka shiga mota suka tafi. Hannah bata iya cewakomai ba sai ta sunkuyar da kai kasa tana kukamalam habu ma kukan yake uwar biyu ta matse hawaye tace'' kuyi shiru, ku daina kuka wannanduk abune na shirme da karya ita wannan yarinyardata zo ina tunanin matar da malam haisam zai aurace take ganin son hanna yake alhali kowa yasanhaisam a matsayin yaya koma ince uba yake awajen hanna tun tana karama fa inah, ai zancen so ma bai taso ba. Hannah karatu take a makarantababu wata soyayya daga wannan hutun ma bazasu sake dawowa har sai sun gama makarantar makwata kwata saura wata bakwai su gama. malam habu ya zabura yace'' wacce komawa aihanne tazo kenan baza ta koma ba ina wanizancen saura wata bakwai hanne ta gama aikosaura kwana bakwai ne hanne ta gama karatuntabayan a gaban mutane aka ce ba karatu take yi amakarantar soyayya take yi sannan in bar yata ta koma ai sai a dinga cewa tana can tana iskanci harwata bakwai ba ta komo gida hutu ba, ni daiabunda zance muku uwar biyu ke da wannan yarohaisam allah yayi muku albarka amma hanna bazata sake koma wa ba karatun ya isa haka dukkawayenta harma da kannanta duk sunyi aure gara itama in hadata da wani a dangi tayi aurentabaki alaikum kafin a kone mata fuska. Damanabunda muke ji a redio gaskiya ne ace an fesawawani ko wata wani ruwa a fuska ya kwakwkwabogaske ne to ba zai faru akan hanne ba. Karatun datayi na baya ya isa nagode madalla'' cikin rudewa uwar biyu tace'' haba malam habu yaya zaka yimana haka ? Baka kyauta masa ba yarinyar nanduk zance take haisam ba zai barta taje gurinhanna ba balle tayi mata wani abu. Bama a barinkowa yaga dalibai in ba ranar bisitin ba dokarmakarantar ce'' malam habu ya mike ya shiga gida yana cewa'' nifa na gama maganata uwar biyu kiyihakuri ki bar maganan komawar hannemakaranta. Ai ko karan hauka ya cije ni ba zan baryata taje inda za'a halakata ba ina hanne ina kishida wadannan gogaggun yan burnin masu kudi.Tunda tana ganin mijinta son hanne yake ai sai a hakura da taimakon na baya ma allah ya saka'' yashige ya bar hannah tana matse hawayen dakeidanuwanta da wani farin hankici dake hannuntatace uwar biyu'' kyale shi ya tsorata ne kafin hutuya kare zai yadda idan na wayar masa dakai ahankali na lallabashi sai dai idan hutu ya rage sati guda kizo don muji mai zai ce in yaki yadda sai daiyaya haisam yazo ko kuma ya turo principal idankuma yaki yarda na shiga uku karshen karatunaya zo. Hannah ta rushe da kuka, uwar biyu tace ''yadda za'ayi shine haisam zan turo yazo garin nanmahaifinki ya kalli kwayar idonsa ya ce ya hanaki ki koma makaranta, haisam zaizo da kansa. A hakahannah da uwar biyu suka yi sallama. Hanna tayitayi da uwar biyu ta shigo cikin gida ta huta sannanta tafi uwar biyu tace baza ta shigo ba ina zata iyashigowa wajen iya abu masifaffiyar matar da zataiya kashe mutum ma don rashin imani. Hannah ta raka ta har tasha ta shiga mota sannan hanna tadawo gida. Zaharaddeen Shomar Whatsapp 08168575100 GANGARJIKINSA NA AURA 1 Part 4 Posted by ANaM Dorayi on 02:25 PM, 30-Apr-15 Under: Gangarjikinsa ta Aura A zaure malam habu ya shimfida tabarmar kaba dawani yagulallen filo da zanin gado irin na da da dadinnan shekara aru aru da suka shude. Nan neshimfidarsa da yake kwana nan ne dakinsa danduk dare duk sanyi da damuna a nan yake sabodaiya abu ta mamaye dakunan gidan. Dakinsa din ya barwa hanna data girma ya dawo zaure don da datana yarinya tare suke kwana a dakin. Ko dayaushe hannah zaka ganta a zaune a gefenbabanta tana lallashinsa tana wayar masa dakaigame da makarantarsu. Tana nuna masamuhimmancin karatu da kuma irin bacin ran da haisam zaiji idan bata koma ba.Ta kwashe labarun abubuwan da suka faru tuntana aji daya har tazo aji shida yadda haisam yakekula da ita da irin tataburzar da aka sha yi akantada dalibai da malamai har ya kwatar mata yancintababu mai dukanta ko zaginta yanzu, kuma yayialkawari zai iya kashe ko waye yake son ya takura mata. Malam habu ya gamsu sosai da bayananhanna ya kuma san haisam ba zai yadda a cuce taba. Hutu ya rage sati guda sai ga uwar biyu ta dira agarin su hanna ta iske hanna da mahaifinta a zaurea zaune zance daya dai suke ta nanatawa kullumshine zancen ya barta ta koma makaranta. Bayansun gaisa da uwarbiyu ta fadi abunda ke tafe da itacewar tazo ne ta tafi da hanna hutu ya kare sai malam habu ya kekashe idanuwansa ya ce shifababu inda hanna zata je. Hanna tayi mamaki da tajiya fadi haka yanzu bayan da ya yarda da tayi masabayani sai kawai hanna ta rushe da kuka, magiyarduniyar nan uwar biyu ta dinga yiwa malam habuamma yaki yarda daga karshe uwar biyu tayi musu sallama ta tafi. Tana isa kazaure ta wuce gidan susafiyanu abokin haisam bata sameshiba ance yanakano sai ta koma gida ta zuba ido ko allah zai jehomata haisam ko safiyanu idan zasu kawo sayayyarhanna ta makaranta tunda sunsan hutu ya karezasu kawo. Har ana gobe a koma makaranta uwar biyu bata ga safiyanu ba balle haisam. A can kuwahanna hankalinta ya gama tashi taji shiru yayahaisam baizo ya taya ta rokar babanta , sai ta daukashima yayi fushi ne yace to a bar masa 'yarsa kartayi karatun mana. Da la'asar likis hanna damahaifinta suna zaune akan lintsimemiyar tabarmar kaba a zauren kasa da rufin ciyawa hanna kukatake yau tun safe. Malam habu lallashin duniyar nantayi shiru ta hakura tama cirewa ranta makarantardon shi ya gama magana bazata koma makarantaba . Taki ci taki sha sai kuka take rafsawa. Kwatsamsuka ji sallama daga idon na da hanna tayi sai tayi ido hudu da yaya haisam , safiyanu da uwar biyusuka yi sallama suka shigo. Da sauri hanna tadauko musu tabarma ta shimfida musu sukazazzauna ta koma ta dauko musu ruwa a randacikin kwanan sha. Ta kawo ta durkusa kasa tagaishe su ta koma gefe ta zauna. Murna ce ta rufe malam habu yama rasa inda zaisa wadannanmanyan baki, yan gayu, ya lalubo kudi a aljihunsaya ce da hannah tayi maza taje bakin kasuwa tasuyo musu fura da nono, su haisam suka ce kaihaba ai su a koshe suke ya barshi kawai. Bayansun gaggaisa malam habu ya gama yi musu sannu da zuwab da tako kare sai safiyanu ya nisayace''baba munzo ne mu ba da hakuri akan dalilinda yasa ka hana hanna zuwa makaranta. Shinemuka zo da kammu mu roke ka baba duka dukasaura wata nawa ne yanzu hanna zata gamakaratunta ta dawo gida'' nan da nan malam habu ya canja fuskar fara'ar dayake ta gushe yace''wai me yasa kuke sani inamuku kin kyautatawa ne ? Bana so ku tambayeniabinda zan kasa baku na gama magana don allahdon annabi ku bar zancen karatun 'yar baba. Nayanke shawara ba zata koma ba. Haisam kokarin da yake yi allah ya saka maka hakan ma ya isa basai ta kara yin wasu watannin ba. Nace uwar biyuta yi maka godiya ka cika min alkawarin da kadauka wallahi ko bata karasa ba ai ka cika alkawariba laifinka bane. Alkawari da amana ai ba karaminaiki bane cika su amma cikin yardar allah ka cika dai dai ubangiji ya saka maka da gidan aljanna.Amma hanna ba zan bari ta koma ba. Haisam yayidan murmushi game da gyaran murya ya ce'' aminbaba, amma idan baka manta ba a ranar dana karbiamanar hanna nayi alkawarin hanna zata yi karatuto kai ma a lokacin kayi min alkawari,kaga alkawari girma ne de dashi baka cika ba, kayi min alkawarinzaka bar hanna tayi karatun don sai dama nasakayi alkawarin zaka dinga turo hanna makarantabaza ka hana ta ba wataran sannan nayi makaalkawarina. Malam habu yayi shiru zuwa wani danlokaci can ya nisa yace'' anyi haka yaro haka akayi nayi maka alkawari to ammma ai abinda yarinyarnan tace gargadi fa tayi min akan kada in kara tura'yata makarantar nan kaga ai kome tayi mata batada laifi nine ban ji ba kenan'' haisam ya katseshiyace'' kare lafiyar hanna da duk wani abinda zaicuce ta yana daga cikin amanar dana dauka in allah yaso babu mai yiwa hanna wani abu. Ramla kuwata fada ne kawai a cikin bacin rai amma babuabinda zata yiwa hanna, a ina ma zata ganta balletayi mata wani abu ? Ta dai fadi son ranta dontatsorataka kaga baba kuma abinda ta fada ba hakabane hanna karatu take haikan a makaranta, kanwa ce hanna a wajena ni ne mai tsawatar matama misali da ace tana soyayya da samari amakarantar . Baba mu canfa akwai doka babuyadda za'ayi malami yayi soyayya da daliba, babukuma yadda za'ayi wata ya shigo cikin makarantardauke da wata guba taje ta cuci dalibai don haka baba ka kwantar da hankalinka ni da kai duk mucika alkawuran da muka daukarwa allah''.Malam habu yace ''to shikenan allah ya taya mucikawa. Hanna dauko kayanki ku tafi allah yakiyaye hanya''suka duka suka ce amin''sai murnata dira a zukatansu. Cikin farin ciki da jin dadihanna ta shiga ta fara hado kayanta ,iya abu tayicaraf ta fito daga bayan kyauren da take labe ta hau malam habu da fada'' au yarda kayi dawannan dadin bakin da suka yi maka. Duk wannangaskiyar data baiyana yarinya iskanci suke amakarantar don yana aiko maka dana goro shinekaki fadar allah saboda abun duniya ? Kallo dayahaisam yayi mata yaga irin wadannan mutane ne masu abun haushi masu kama da aljanu munanamasu bakin hali yaji ya tsani iya abu har baya so yakara kallon fuskar shegiya. Hannah ta ratayajakarta ta fito ko kallon iya abu bata yi ba balle tayimata sallama. Ta duka ta yiwa babanta godiya tayimasa sallama ta wuce cikin mota. Haisam ya danko kudo mai yawa ya ajiye a gaban malam habu.Safiyanu ma haka ya debo kudi ta ajiye masa sukayi masa sallama dukkaninsu yana godiya sunagodiya suka shiga mota suka tafi. Ba safiyanu bahar haisam yaji ya sake tausaya rayuwar hannasaboda ganin yadda gidansu yake. Gidan kasa ne anyi masa katanga da kara rufin azara abin dai abintausayi talauci dai tsagwaransa. Babu abinda zakadaga a gidan ka sayar dashi dari biyar komai ragaraga kaico!hannah na komawa makaranta tasalittafinta a gaba tahau karatu. Sune yanzu masushirin zana s.s.c.e don haka babu wasa sai karatu. kwance tashi su hannah sun fara jarabawarsu takarshe [s.s.c.e} saboda daman tuni sun gamatsarge karatu. Sai suka ga cin tuwo yafi jarabawarwuya sai kawai suka hau fede ta. Geography dinmalam haisam itace wacce suka yi ta karshe damisalin karfe hudu na yamma suka gama daman jakunkunansu su suna baki hall din da sukejarabawar suna fitowa sai kowacce ta dauki jakartasai tafiya daman kowacce ta kagu taje gida taga'yan gidansu basu taba irin wannna dadewa amakarantar ba har watanni bakwai a makaranta.Hatta hanna da bata so ayi hutu itama yanzu so taje gidq taga mahaifinta sai mafarkinsa take kullum takwanta barci. Hanna da kawayenta sun sha kukanrabuwa musamman ita da nusaiba sun saba sosaigashi zasu rabu. Gashi kuma babu waya a garinsuhanna balle su dinga gaisawa a waya. Rauda ma tarungume hanna tana kuka taji duk babu dadi yanzu da zasu rabu kuka wiwi juniors suke yi narabuwa da seniors dinsu zasu tafi su barsumusamman hanna basu ji dadin rabuwa da ita basaboda tayi musu mutunci samun shugabar dalibaiirin hanna sai an bincika. Ta koya musu abubuwana cikin kungiyoyinsu {club}na makarantar. A haka kowacce ta tafi gida kuka wiwi. Safiyanu ne yazo yadauki hanna ya kaita gidan uwar biyu. Yau haisamtun kafin su shiga jarabawa yazo yayi musu sallamaya koma gidansa ya rufe kansa kansa ko wajen daake bankwana bai zo ba saboda tsananin bakincikin rabuwa da yan ajinsa da yake matukar so. Gidan uwar biyu ma sai washe gari yaje ya samuhanna a can. Bayan sun gaisa ya ce da hannah''yau zaki tafi gida ko sai kin sake hutawa kamar satidaya anan sannan ki tafi ? Hannah tayi caraf tace''yaya haisam yau zan tafi na dade banga babanaba'' haisam yayi dariya ya ce'' wato ke yanzu kin bar kazaure kenan zaman kazaure sai mu ? Tayidariya tace'' sai ku ai mun daku wannan hutun harna daina sha'awar garin allah yaya haisam'' haisamya mike ya ce'' to ki shirya zanje nan makwabtasafiyanu yana ciki wajen abokansa ana wankemasa motar ana gamawa sai ku fito zan aiko yaro yayi kiranku sai mu kaiku tasha ku tafi. Da har cangarin zamu kaiku inyiwa baba godiya ince masagaki na dawo masa dake lafiya na cika alkawarishima ya cika to sai safiyanu ya ce kano zai tafi dakakarsa in anjima'' hanna tayi dariya tace'' kai yaahaisam ai babu komai yana gani na yasan lafiya na dawo lallai kuwa ka cika alkawari'' ya juyo yakalleta yace ''ko? Tayi murmushi tace'' E'' sannan yafita yana murmushi. Bayan fitarsa da dadewa sosaiyaro ya shigo ya ce wai uwar biyu da hanna su fitoinji su safiyanu suna kofar gidan dallatu'' daman ashirye suke tsaf sai hannah ta dorawa yaron jifgegiyar jakar kayanta. Jakunkuna uku ne. Yakaiya dawo ya dauki ta biyu sannan yazo ya dauki takarshe sannan suka fito uwar biyu ma da buhuntaa kanta, suka shiga mota sai tashar kazaure.Hannah ta hado kayanta kakaf na gidan uwar biyu.Katifa da bokiti kuwa taba uwar biyu kyauta. Kaya masu kyau atamfofi da shaddoji da yawa. Hanna tabawa uwar biyu kyauta da 'yarta halima. Dake kayatsadaddu leshi ma uku, shadda da atamfofobibbiyu yaya haisam ya yiwa hannah na candy.Bayan takalma da yan kunne, sarka da dan kunneharda gwal ya suyo mata. Suna isa tasha a bakin tasha safiyanu ya tsaya da motar. Ma'aikata nan'yan union su biyi suka zo suka tambaye su inazasu da suka fada sai suka ce babu motar babbanmutum yanzu amma baza a dade ba zata zo. Haisamyace su kwashe jakunkunan su kai cikin tasha,hanna da uwar biyu suka shiga cikin tasha. Safiyanu da haisam suna nan bakin mota a tsaye abakin tasha. Can suna taye suna hira sai safiyanu yakalli agogo ya ce yanzu fa muka yi da hajja kakatazan dawo mu tafi kano tana can tana jira na''haisam tace'' ai ba komai heka kawai nima idannaga tafiyarsu acaba zam hau in koma cikin makaranta.. Suka yi sallama safiyanu ya shiga motaya tafi, haisam kuma ya shiga cikin tasha A cikinwata yar rumfa ya iske hannah a zaune akan jakarkayanta uwar biyu kuma akan wani benci suna'yar hira suna jiran zuwan mota.Haisam ya karasa cikin yar rumfar yanatambayar su''har yanzu motar bata zoo bane? Uwarbiyu tace'' sun dai ce yaznzu zata zo munzo da wurine wai daman motar bata zuwa da wuri'' ta mike dasauri daga kan bencin tace da haisam ya zauna ,yace''lah babu komai yi zamanki mana''' uwar biyu tace'' a'a ka tsaya'' ga kawayena acan suna sayarda zogale bari inje wajensu mu gaisa daman dankar na bar hannah ita kadai shine yasa banje tundazu ba''uwar biyu ta tafi .haisam ya zauna yanakallon matafiya da masu mota ana ta hayaniya. Canya juya ya kalli hanna wacce ke zaune akan jakarta tayi jugum kamar tunanin wani abu take, ya kuramata ido kawai yana tunani a ransa. Babu abundaya fara tunawa sai a ranar da aka fara kawohannah makaranta ta ci dammara ta hau ta zaunaakan akwatinta tayi jugum tayi shiru a lokacin dababanta ya tafi ya barta. Amma yanzu maimakon dammarar da taci sai tayi shar da wani tsadaddenbakin leshi mai duwatsu kala kala suna sheki ajikinta. Dinkin fitet tsamammiyar riga da siket ta yafadan yalolon gyale ta dana daurin dan kwali yayinda lallausan gashin nan nata mai santsi baki datsawo ta tufke da bakin ribon a keyarta. Hannah ta dago kai sai taga yaya haisam kallonta yake yikawai a lokaci guda sai kowannensu ya sakarwadayan murmushi. Abunda itama ta fara tunawaranar da babanta ya kawota makaranta ta hau kanakwatinta ta zauna tayi shiru yaya haisam yanazaune akan benci yana kallonta. Mai tallar biredi ne yazo ya ishesu da a sayi buredi ga gardi, zakibiredin tsaraba . Haisam ya kalli hanna yace'' bazaki sayi abun tsaraba ba ne ki kaiwa yara? Hannatace'' kyalesu yaya'' ya ce '' ban gane kyalesu ba,haka zaki yi wata bakwai kije musu hannurabbana, biscuit ko sweat zaki shiga aishalle ki saye, ungo kudin ko ki aiki wani yaron? Ya cirokudi a aljihunsa, hannah tayi dariya tace'' su fasunfi ganewa ayi musu tsarabar biredi'' haisam yace su sha tea da safe dashi ? Hannah tace'' a.a surinka gutsira a haka'' su duka suka yi dariya.Haisam ya ce da mai biredi ya sauke yaje ya siyo jakar bacco ya dawo. Ba dadewa sai ga mai biredidauke da jakar bacco. Haisam ya ce ya juye buredinduka a ciki. Hannah ta rike baki tace'' yaya haisamwadanna manya manyan buredi har wajen takwasai suna da girma sunyi yawa biyu ma sun isa''haisam ya ce a'a basuyi yawa ba kowa yazo yayi miki sannu da zuwa sai ki yago masa gayan birediki bashi kice tsaraba'' su dukkansu suka kyalkyaleda dariya harda mai sayar da biredi dadi yakamashi ana masa ciniki. Mai lemon fata ne yagarzayo da sauri yaga an siye na abokinsa, shimaya bude muryarsa gaba daya yana ''a sayi na tsaraba'' shima haisam yace ya siyo bacco yazo yajiye duka farantin , yayi kololo kuwa dan cika. Nada nan ya garzaya da sauri ya siyo bacco ya juye saikudinsu tumus a hannu. Sika jerawa hannabakkuna a gaba suka tafi suna murna. Hanna tadago kai ta kallo haisam fuskarta cike da murmushi gami da nuna jin dadin kulawar da yake yi matatace'' yaya na gode fa kwarai da gaske'' ya ce''babu komai hanna'' hanna ta dago ta kalle shi sukahada ido tace'' yaya haisam baka bani abin busanaba da tsakiyoyina daka ce in baka zaka boyeminkada malamai su kwace min din nan tun randa aka kawoni aji daya.Haisam ya tuntsire da dariya hanna ma hakayace'' bazan baki ba sai kinyi wannan kwalliyar dakika yi a fuskarki mai digo digo nan da wannandammarar da kike yi sannan zan baki sarkokinki''suka sake tuntsirewa da dariya ya ce'' busa nake yida abun busarki fa. Kusan kullum da daddare kafin in kwanta zaki yi mamaki idan aka ce yanzu na fikiiya busar da wakar. Nafa rike yadda kuke wakarda amratu kanwata zabje in kaiwa a gida ashe bakibani ba, bari inje in dauko muki'' hannah tayi sauritace'' ban san kana so ba na bar maka, hartsakiyoyin ma in so kake? Yace ''eh suma amratu zan bawa ta dinga kwalliya dasu'' hannah tayidariya tace''amratu baza tayi kwalliya dasu ba,komu yan kauye mun daina saka irinsu'' motar dazata je babban mutum ce ta shigo. Doguwar bus cenan da na uwar biyu ta taso tace dasu'' hannah gamota nan tazo daga jakar su zuba kayan a but'' kwandasta yazo ya debi jakunkunan kayanhannah da tsarabar ya zuzzuba a but, hannah dauwar biyu suka shiga kujerar baya su biyu kacalsauran wajen haisam ne yake biya daman hakayake musu in dai ya kawosu tasha to mutane hudubasa zama a baya. Hannah da uwar biyu ne kawai suke zama ya biya kudin sauran kujerun. Matafiyasuna ta shiga mota haisam yazo ta jikin wundonuwar biyu ya mika mata kudaden motarsu dakuma wanda zata bawa mahaifin hannah kamaryadda ya saba aika masa, uwar biyu tana ta godiya.Haisam ya zaga ta wundon hanna wacce jikinta yayi sanyi tana daf da fashewa da kuka, ya mikamata wata ambulam fal da kudi. Ya fara yi matanasihohi masu tsuma zuciya kamar yadda ya sabayi mata amma wannan karon nasihohin sunshabambam da na kullum hade da bankwana yake yiyace'' hanna alhamdulillah allah ya kawo mu ranar da kika gama makaranta kin zana jarabawarkarshe allah ubangiji ya baki sa!a. Hanna ki kula daaddininki sosao daman can ke mai addini ce nasanda haka amma ki kara . Kada ki damu a duk halinda kika tsinci kanki. Na wahala kina jin dadi dukallah yana sane dake kuma yana sonki ba wai ya wareki bane don ya tsaneki yake hadaki da masifuiri iri da bakin ciki. Allah {s.w.a}yana jarababawansa ta duk inda yaso kiyi kokari kicijarabawarki , ki kuma din ga gode masa a dukrintsin da kike ciki. Idan kika gode masa a dukyanayin da kika godewa allah to shi zai canja miki, ina so ki kula cewar babu wani mutum a duniya dazai zama shine matakin gatan kowa don allah kirike wannan allah shiya halicce ki shi yake ba dawakuma shi yake hanawa babu me miki wani abubanda allah kici gaba da yin tawakkali allah yanasane dake. Tsananin kukan da hannah take rusawa shine ya dabartar da haisam ya rasaabunda zai ce shima ji yayi kwalla ta cika masa idotaf sai kawai ya juya ya tafi ya ce'' allah ya kiyayehanya, sai anjima'' wani kululun bakin cikin neyazo ya tokaresu dukkansu a wuya tsananin bakincikin rabuwa da juna. Gagarumin tashin hankali ya mamaye zukatansu kowanne na fidda ran sakeganin dan uwansa kuma. To tayaya hanna zata zokano tace tazo ta gaishe da malaminta bayan ramlana nan na nemanta zata halakata idon ta idon tatace sai taga bayanta. Shi kuma yaya za'ayi haisamyaje garinsu hanna bayan duk gari ya dauka sharrin da ramla tayi, iya abu na yadawa hanna bakaratu take yi ba soyayya take yi da wanimalaminta. Hanna tayi zugum a zaune a mota ji takeduk duniyar babu dadi. Yanzu zaman dindindinzata je suyi da iya abu tasan ba karamin bakin cikizata hadu dashi ba a gidan. Ga tsananin bakin cikin rabuwa da yaya haisam saboda sun saba sosai dontafi jin bakin cikin rabuwa dashi akan nusaibawacce suke kwana tare su tashi komai tare hattabacci baya rabasu. Uwar biyu ma sai duk jikintayayi sanyi shi kenan idan ta kai hanna gida baza tadawo ta dauketa ba kuma. Suka isa gidan su hannah, hannah ta shiga gida da sauri tana murnazata ga babanta. A shimfidarsa a zaure ta ganshikwance sharkab babu lafiya ashe watansa wajenhudu a haka. Ciwo kullum gaba yake sake yi saiakwantar a tayar. Hannah ta gigice har tana nemanrasa hankalinta yayin da taga mahaifinta ya zama kashi a kwance kurket dashi kaninsa ne uwa dayauba daya yazo yana jinyarsa . Dan ta iya abu cewatayi ya mutu mana tace ta gaji da zaman jinya tundayaki warkewa tayi na allah 'yan uwansa kuma suzosuci gaba da kula dashi ita ta huta. Hannah tasakuka taje ta tsugunna a gabansa tace'' sannu baba'' yace'' yauwa sannu 'yar baba ashe da rabonkizo muyi magana ban mutu ba nace aje a kirawomin ke a makarantar kizo kiga gawar mahaifinkibasu je ba'' cikin sheshshekar kuka hanna tace''baza ka mutu ba baba daina fada ma'' uwar biyuma ta matso kusa dashi tace'' sannu malam habu ya jikin ''yace'' jiki dai gashinan uwar biyu sai dai kuyimin addu'a idan na mutu, allah ya saka miki daalheri ke da haisam da gidan aljannah abundakuka yiwa hanne na gode''uwar biyu ma hawayetake yi. Hanna tayi kuka kamar ranta zai fita. Ananuwar biyu ta yini sai da la'asar tace zata tafi suka yi sallama da malam habu dake radai yana maganatashi tsaye ne baya iya yi. Hannah ta rakata hartasha.A hanya Uwar biyutakebawa Hannah shawara ta ce "Tun da ke mai ilimice kiyiamfani da iliminki, ki kai Mahaifinki asibitin Baburatunda kudin da Haisam ya bawa Mahaifinki dawandaya baki mai tsokane zai isheku. Da abarshi a gidaanamasa jike-jike duk wata cuta ake kara masa.Mutum akwance har wata hudu ya kare sai kashi da fata. Atashar Uwar biyu ta sami mai mota aka yi tsadazata jegida a dauko marar lafiya a kaishi asibiti. HannahdaUwar biyu suka shiga mota, dake itama Uwar biyudaman motar Babura zata shiga daga Babura zatahauta Gumel. Sai kawai su duk su tafi tare. Motar tajeharkofar gidan, direban da kwandasta da kanin MalamHabu suka ciccibeshi suka sashi a mota sukashigasuma da *yan kayayyakinsu suka nufi asibitinBabura.Iya Abu nata yiwa Hannah surutu tana cewa gatananUwar iya yi wai har tayi kilin din da zata daukiMahaifinta ta kai asibiti wai har asibitin Babura tazama *yar boko. Sai da Uwar biyu tayi wata gudacur aGumel sannan ta dawo Kazaure tana zuwa tananiyyarta shaidawa Haisam halin da Mahaifin Hannah kecikisai aka ce mata ai bayan tafiyar su Hannah da satibiyushima ya bar koyarwar ya kwashe kayansa yakomaKano. Ta nemi Safiyanu shima aka ce mata ai shitundayayi aure a Kaduna ya tare da sabuwar amaryarsaacan ya sami aiki, sai Uwar biyu ta hakura dasanarwaHaisam don ita bata taba zuwa Kano bama balleta tafinemansa. Su Hannah kuwa sai da suka shafe wataguda da kwana shida sannan aka sallamesu dagaasibiti. Kanin Mahaifinta ne a wajensa amma itamatakan je tayi kwana biyu uku acan har dai sukadawogida gaba daya. Jiki da sauki tunda yana zama dakansa ba sai an tallafo shi ba. Sai dai kudadenhannunHannah sun kare kakat saboda siyan magungunanasibiti.Nan fa balokokon Iya Abu ya tashi akan tagaHannahbata da kudin da zata sayi dan biskit da madarardatake sha idan tazo hutu da, dole ta ci tuwan gidan.Hannah ce shara, wanke-wanke da dafa abincitukatuwan bakar dawa da miyar kuka a murhun kasa.Kwanci tashi su Hannah sunyi wata biyar da gamamakaranta. Hannah har ta fara zuwa makarantarbokongarinsu tana koyarwa. Duk da dai ba'a dauketa amatsayin Malama ba don Jarabawarta bata fitoba.Amma a karshen wata ana bata dan na batarwa.Ranarasabar babu makaranta. Da sassafe bayan Hannahtagama wanke-wanke tana kokarin daura tukunyartuwon burabuskon gero miyar kuka na rana saikawaiIya Abu tazo ta kashe wutar da ruwan tuwon. Tace tacanja ra'ayi yau an fasa yin abincin ranar sabodaunguwa zata ita da jikokinta don haka meyeamfanintuwon. Ta dauke garin tuwon da kukar kadin tasaadaki ta datse ta yafa mayafinta zata fice. RanHannahya baci ta ce "To Baba fa, me zai ci shi da bashidalafiya? Yau jikin nasa a rikice yake tunda sassafeamaiyake. Iya Abu ta ce "Sai yaci hakuri ko ki kwasheamanda yayi ki dumama masa. Cikin fushi Hannah ta ce"Inaraye a duniya Mahaifina ba zaici amai ba inshaAllah"Mari tas Iya Abu ta sakar ma Hannah akanlallasusankuncin nan nata ta ce "Ke kin isa ina fada kinafadalalle wuyanki ya isa yanka. Malam Habu da yakekwance sai jikinsa ya dau kakkarwa tashin hankaliyadira a zuciyarsa yaji marin da aka sakarwa Hannesaiya hau hawaye yana kira "Yar Baba yi hakuri zonanwajena ki zauna. Hannah tana hawaye ta je gefenshinfidarsa ta zauna Iya Abu tana tsaye akansutana tabalokokonta tayi har ta gaji ta kama hannunjikokintasuka fice, da taji ba'a kulata ba. Zuwa can wanilokacimai dan tsawo Hannah da Mahaifinta sunyi zugumsuna tunani sai ta jiyo mai tallar fura da nono tazotazo wucewa, da sauran *ayan canji a jakarta tatashita leka ta kirawota, ta dauko kwanon sha ta saya.Tadama ta tashi Mahaifinta zaune ta bashi yasha yakoshisannan ta gyara masa kwanciyar ya kwanta takomagefensa ta zauna tayi lamo zuciyarta cike datakaici gayunwa tana addabar cikinta. Can Malam Habu yace"Yar Baba, ta ce "Na'am Baba. Ya ce "Allah Yayimikialbarka ya baki miji na gari mai sonki kamarHaisam,sai Hannah tayi shiru tana tunani da mamaki yaakayiMahaifinta yake hada mijinta da Haisam.Malam Habu ya ce "Ya ba ki amsa ba? Ta ce"Babakamar Haisam kuma? Ya ce "Eh kamar yadda yakekuladake yake nuna miki kauna. Tayi murmushi ta ce"Mutunci ne dashi da tausayi amma ba soyayyabace.Malam Habu yayi dan tari ya ce "*yar Baba matsokusadani kiji. Hannah ta matso kusa dashi. Ya ce "YarBabababu mai sonki a duniyar nan kamar Haisam, babumairikeki tsakani da Allah irin Haisam, babu mai rikekiamana ko bayan raina wanda ko dar bana yi saishi*yar Baba. Haisam yana matukar sonki. Hannah tace"Meka gani kake cewa haka? Ba sona yake ba kokadanmutunci ne ai bai taba gaya mun ba. Malam Habuyanisa ya ce "Yanzu tashi kije ki nemi gidansu aKanokice na amince masa ya zo zan bashi ke ya aureki.Hannah ta zabura ta ce "A'a Baba ya za'ayi injekawaiince masa ka yarda yazo ya aure ni bayan bai cezaiaureni ba. Malam Habu ya ce bakya yimun musu,karkifara daga yau bazan ce kiyi abunda zaki cutu bajekikawai ki fada masa. Haisam ne zai rike mun keamana*yar Baba duk duniyar nan shine kadai na yaddayaaureki. Jeki ki shiryo ki tafi yi sauri *yar Baba.Hannahta tashi a sanyaye zuciyarta cike da zuluminwannanal'amari.Ta shiga cikin gida ta sake salla wanka ta sakawanidandatsetsen sabon leshinta kalar brown ta yafagyalenta a kusa da Babanta ta ce "Na shirya zantafi,ya laluba karkashin tabarmarsa ya dauko wasukudi yabata, ya ce tayi kudin mota. Ta ce ya barshi tanadakudin mota, ya ce ta karba shi mai zaiyi da kudininbata karba bama kwashe su za'ayi, kudin da yatattarane na *yan dubiya. Har Hannah takai bakinkofazata fita sai ta tuno ai bata san kwatancen gidansuHaisam ba gashi bata taba zuwa Kano ba sai cantatuna akwai inda ya rubuta mata kwatancengidansu ajikin littafinta (slum book) da ta bashi ya cikemata. Takoma daki da sauri ta binciko cikin littattafanta tadauko sai kawai ta jefa littafin a jaka ta fito.MalamHabu na kwance bacci ya fara daukarsa yajimotsinmutum sai ya bude ido ya ce "Waye? Hannah tace "Nice Baba, ya ce "Baki tafi ba ne, *yar Baba kobakyasonzuwa ne? Ta durkusa a gabansa ta ce "Baba bahakabane mantuwa nayi na dawo amma yanzu zan tafizanbi ta gidan Iya Salma(tsohuwar matarsa ta fari) koitatazo ta taya ka zama kafin in dawo baza a barkakaikadai ba. Malam Habu ya ce "To Allah Yayi mikialbarka. Hannah ta ce "Amin Baba Allah Ya bakalafiyaya ce "Amin *yar Baba, kuma ko bayan raina adauraaurenki da Haisam ina fatan kema kina sonsa?Hannahtayi dariya ta rufe ido, alamar kunya Malam Habuyayidariya shima ya ce "Yar Baba fada min gaskiyamana.Ta ce "Baba saboda tsananin kyautatawa da kuladayake mun sune suka sa nake ganin girman YayaHaisam har naji babu wani mutum da nake so datsananin kauna bayan kai Mahaifina sai kuma shi.Babaina son Yaya Haisam sosai har nakan kasa bacciyanzusaboda tunaninsa da kewar sa musamman yanzudamuka rabu. To amma Baba babu yadda zanyi sainagakamar shi ba haka yake nufi a zuciyarsa ba.MalamHabu ya ce "Tashi kije shima yana sonki fiye dayaddakike ji. Amma muyi addu'a kafin ki tafi mu karanta salati goma gaannabisuka karanta suka shafa. Hanna tadinga kwararo addu'ai sannan daga karshe sukashafa. Hannah ta sake yi masa sallama ta fita. Tanafita gidan iya salmai ta nifa ta shaida mata abundake tafe da ita. Nan da nan iya salmai ya zari gyalenta ta nufi wajen tsohon mijinta dan uwanta abunkaunarta wacce dole ce ta raba su don ta kuladashi kafin hanna ta dawo. Hanna na isa tasha tatarar da mota fijo zata je kano ta cika saura wajenmutum daya tayi sauri ta fada sai tafiya. Babuabunda hannah take ji a ranta yau sai tsananin farin ciki, ji take kamar anyi mata albishir da gidanaljannaj. Tana san yaya haisam har ranta, to shimakuma yadda ta lura yana sonta sosai kuwawadannan dara daran idanuwan nasa ne takehangowa a zuciyarta idan yana kallonta. Da wasufararan hakoransa tasa idan yana mata nasiha wai waya ganni a kano yau a kusa da yayana haisamkuma ma wai yazo muyi aure an bashi ni'' hanna kefada a zuciyartaDadi marar musali ya disu azuciyarta kowa yaga hannah yasan tana farin ciki ayau. Sun isa kano lafiya a tashar yan kura akasassauke su. Hanna ta fito daga mota ta kalli gabas da yamma kudu da arewa. Daga bil'adama neburjik a gaba da bayanta. Tace a ranta''ikon allahkano mai mata da maza, ta dawo tumbin giwa kodame kazo an fika. Yanzu ina zan fara dosa gabas koyamma ? Abunya bata mamaki ganin yadda akekallanta har wasu mazan waiwayenta suke . Da farko ta dauka kowa ya ganta yasan bakauyiya cebata taba zuwa kano ba, ta fita daban da yan garisai da taji wasu samari su biyu sunxo wucewasunce mata'' ke kyakykyawa dan rufe fuskar nantaki kada kisa wasu mazan suyi hatsari a garinkallonki. Sannan ta yarda tsabagen farin da suka gani da kyakykyawan fuskar da kirarta suke kallosai tayi sauri ta dora gyalenta aka ta rufe fuskartaidanuwanta kawai a bude, tace a ranta dukkyawawan matan garin nan daman har wani kyauzaus gani? Kwalelensu yaya haisam ya riga su. Tabude jakarta ta dauko littafin da adireshin gidansu haisam ke rubuce ta karanta sunan unguearsuleman cresent, sai ta sami wani kwandasta motatace malam don allah ina motar suleman cresent ?Yace ''a'a gaskiya babu takamaimai motar da takezuwa irin wadannan manyan inguwanni, ammashawarar da zan baki ki sami tasi ki dau shata ya kaiki har kofar gida. Ga masu tasi nan a tsatstsayebabu kowa a ciki. Ya nuna mata su, tayi godiya takarasa wajensu, babu abunda ta fara hangowa saiwajen waya an rubuta'' make your call here'' takarasa wajen masu wayan tace'' anan ake yinwaya ? Mai waya yace eh nan ne. Ta dauko littafinnan ta dubo lambar nusaiba ta mika masa.Bugu daya wayar ta shiga ta fara ringing. Watamata ce ta dauka sannan ya mikawa hanna kanwayar hanna ta karba tana kallon kan wayar donita baya san yaya zata yiba'' mai waya yace kudinkiyana tafiya an dauka fa kisa a kunnenki kiyi magana. Sannan hanna ta tuna yadda taga ana yibayan ta gaishe da matar sai tace'' hanna kawarnusaiba ce. Nusaiba nake nema'' matar tayi dariyatace'' oh hannah ce ? Nice mami mahaifiyar aiyanusaiba ai tana london har ma an samar mataaddmision tana jiran sakamakon jarabawarta ne ta fara karatu. Hanna tayi bakin cikin rashin samunnusaiba a waya sai suka yi sallama ta mikawa maiwaya kan wayar. Yace''minti uku kika yi. Tace nawane? Ya fada ta dauko ta bashi sannan ta juya ta tafimurna take kawai a zuciyarta yau gata a kano tanawadaka da komai irin na yan burni har kan waya yau ta rike lallai. Wani mai tasi inyamuri baya jinhausa ta samu sai suka fara yarawa da turanci .Tace suleman cresent zai kaita ya fadi kudin ko ragibata nema ba ita a tunaninta komai a burni a kaideyake ba'a neman ragi kuma ita burinta kawaiyakaita taga haisam. Suna shiga unguwar saita dauko littafin ta duba lambar gidan ta gayawadireban ashema a kofar gidan suke sai yace to ai gagidan ta zaro kudinsa ta bashi ta fito daga motar yaja motars ya tafi. Tsantsari, wani tsalelen gida negidan su haisam yafi duka gidajen layin tsaruwahanna tayi matukar mamakin ganin gidan su haisam saboda bata taba zaton haisam dan gidangawurtaccen mai kudi bane irin wannan .wasutsala tsalan motoci tagani a wajen get din gidan sundosho goma. Ta tafi kofar gidan makwabtansu tazauna akan wata kwalbati tana tunanin yaddaza'ayi yau taga haisam,Wani buzu mai gadi ne ya leko ta jikin get yahango hanna a kofar gidan da yake gadi sai yayiwuf ya fito yace'' kai me kana yi anan ? Tace''waninake nema ''yace waye wani, ba zaka tambaya bazaka zo ka zauna anan! Hanna tace''haisam nacangidan. Yace''kace na can gidan me yasa kazo nan ka zauna kuma, kaima bakauye ne ko? Don kayikama da yan garinmu masu yalalo yalalo gashi'' saisu duka suka yi dariya shi da hanna'' mai gadin yaleka kofar gidan su haisam yaji hayaniyar mutanesai ya ce mata'' yauwa ga haisam din can sun fito itada abokanayenta''hannah yace'' dan allah dan garinmu kirawo min shi akwai maza bazan iyazuwa ba. Buzu ya karasa wajen haisam ya shaidamasa wata na kiransa. Haisam cike da mamaki yatunkaro wajen da hanna ke tsaye sai tasa gyale tarufe fuskarta. Ya karaso inda take a tsaye yayi matasallama ta make murya ta amsa. Yace wacece? Hanna ta sake make murya tace bakuwa ce''haisam ya hada girar sama data kasa yace'' wai kewacece in ba zaki fada ba zan koma ina da abunyi''hanna ta yaye mayafin a hankali ta bude fuskarta.Wai, kamar wanii hasken walkiya ne ya haskewahaisam ido da yaga fuskar hanna ,cikin fara'a da mamaki haisam yace hanna! hanna! Kece!! Tayilallausan murmushi tace'' yaya haisam nice'' taduka ta gaisheshi. Taga haisam ya caba ado dawata babbar riga mai aiki a wata tsadaddiyarshadda fara sol yasa bakin takalmi da bakar hulayayi matukar kyau. Tayi dariya tace''yaya haisam yau kaine da babbar riga ? Har kafi kyau haka'.Yace haba? Tace allah'' yace yaya su baba. Dasauran yan gidanku? Tace sunanan lafiya sunce nagaisheku. Yace to zaki shiga cikin gida ku gaisadasu hajiya'' hanna ta dan yatsune fuska tace'' kaisai dai watarab bi kunya nake ji kuma sauri nake sai dai idan na dawo. Yace daman ba nan kikazobane? Hanna tace ''ni kuwa wa gareni a kanoidan ba kai ba? Gurinka nazo baba ya aikonihaisam yace to gani fada min aiken. Zumudin yajiabunda aka aiko ta ya kama haisam. Tayi shiru tahau rufe fuska. Cikin zumudi haisam yace'' haba hanna ki fada mun mana kunyar me kike ji ne?Tace'' baba ne yace inzo in fada maka cewar kazoka nemi aurena ta bakani. Tu kafin ta karasa saitaga haisam ya fara dariya da alama farin ciki yacika zuciyarsa. Ya kurawa hannah ido na wani danlokaci yqce'' abunda kika kasa fada daman? Ya sake yin dariya ya tsaya kallan hanna wacce takerufe idanuwanta saboda kunya ga tsananin farinciki.Haisam ya nisa yace''yanzu baba da kansa yacekizo ki cemun ya bani ke! Hanna ta amsa da''eh''yace yanzu ya bani ke kacokan a matsayinmatata? Yanzu baba ya yarda ki zama uwar yayanamun zama daya dangina sun zama danginki,iyayena sun zama iyayenki? Yanzu baba ya yarda na zama abokin rayuwarki na dindindan har abada? Yanzuhanna kin amince zaki zama abokiyar zamana harabada? Hanna cike da fara.a da murmushi takeamsawa haisam tambayoyinsa da ''eh'' haisam yayimurmushi ya sunkuyar da kai na dan wani lokacican ya dago ya kurawa hanna ido yayin da kowannensu yake sakarwa dan uwansa murmushida wasu masun kauna da suke firfitowa dagaidanuwan kowannensu suna yiwa junansu wanikallo mai kunshe da so, kauna muradi ganin juna.Haisam yayi ajiyar zuciya ya nisa ya ce alhamdulillahhanna na daukarwa allah alkawari ba xika , sannan na cika burina dana kudira akanki na ingakin kammala karatunki. Kuma yanzu na dawo gidazan cika wani tsohon alkawari dana dauka. Nan danan hanna ta kurawa haisam ido ta dainamurmushin da take alamar bata gane abundahaisam yake cewa ba. Haisam ya ce'' hanna na gode madalla , ki yimun godiya a wajen mahaifinki .Good bye, good bye hanna. Ya fara jada baya yanadaga mata hannu yana yi mata murmushi . Bakintaya hau rawa tana so tayi magana ta kasa . Gabadaya jikinta ya hau karkarwa inda jakar dakerataye a kafadrta ta sulmiyo wasu marokane suka wayar mata dakai akan abunda haisam yake nufisuna cewa'' ango haisam kasha kamshi fari maifarar aniya kagaa ango na ramla, yan boko bayinnasara a daura aure lafiya akai maka amarya gidalafiya. Wani abokinsa ne ya taho da sauri yace dahaisam ''ana ta yin waya daga wajen daurin aure ance waje ya cika kai ango kawai ake jira.muje ka shiga nota mu tafi mana. Haisam daabokansa suka shiga tsala tsalan motocinsu sukazo suka wuce hannah anan a tsaye tana karkarwaido da ido suke hadawa da haisam har suka wucesuka tafi. Ta juya tabi motar da kallo har suka hautiti suka kure. Sai hanna ta tsugunna a wajen ta rushe da wana azababben kuka mai radadin fita.Dakyar buzu mai gadin nan ya dinga bata hakuri tadauki jakarta dankwalinta a hannu sai gyalenta tayafa a kai ta tafi. Acaba ta hau har tashar yan kurawannan karon ma taci sa.a tana shiga mota ta cika .Kallo daya zaka yiwa hanna kasan hankalinta a tashe yake matuka don kwandasta sai da yayimagana sau uku yana cewa ta bada kudin motartabata jiba, hankalinta yana can tana tunanin damanhaisam ba sonta take ba. Ramla yake so shine ita damahaifinta suke yaudarar kansu . Yaya haisam meyasa kayi min haka me yasa baka fahimci son dana ke yi maka ba ? Ta nisa tace'' ko da yake bashi dalaifi bai yaudare ni ba, ya taimakkamin ne sabodaallah ni na dorawa rai sonsa. Bai san ina yi bakuma, amma na rabu da farin cikin rayuwa na rasamutum na farko dana taba hi inaso a rayuwata,gashi tun bayan gama makarantarmu ko bacci ma neman gagarata yake na kwallafa raina datunaninsa da tsananin sonsa'' sai da wata mata takusa da ita ta tattabta sannan hannah ta farfadodaga tunaninda take yi. Kwandasta yace kudinmota nake tambayarki kinyi shiru kina tunani''sannan hanna ta zabura ta dauko kudin mota ta mika. Mota ta bar cikin kano ta kama hanya fetal saibabban mutum. suna isa babban mutum tun dagatasha hanna ta dinga jin faduwar gaba kafartakamar bazata iya daukar ta ba dakyar take jefakafar burinta kawai ta isa gida taje ta fada jikinmahaifinta ta sharbi kukanta son ranta tunda duk duniya shine kadai ya rage mata gaba dabaya.kamar yadda data shiga kano taga mutanengarin suna ta kallonta har da waiwaye yanzu ma agarinsu haka ta gani sai kallonta ake tana tafiya harda masu nunata kamar basu santa daba, hanna tayimamakin irin wannan kallo da ake yi mat tace a ranta'' to ko sun san son maso wani nake ? Wandanake so yayi aurensa da wacce yake so'' kallon nandai da ake yi mata ya daure mata kai. Haka daihanna taci gaba da tafiya tana sauri ta karasa wajenmahaifinta shine kadai mai lallashinta, mai gayamata kalaman da zata ji dan sanyi a ranta. Ta kusa kofar gidansu, kwatsam taga wata kungiyar mazadauke da gawa sun yi gabas ana hailala. Tajigabanta ya fadi ta dubi kofar gidansu sai taga taronwadansu maza da yara a zazzaune ana jan carbitace a ranta'' ba dai gawar babana bace waccan?Sai ta zubar da takalmanta da jakarta ta shiga gida da gudu don ta duba zaure shinfidar babanta yananan kuwa. Tana shiga sai taga shimfidar wayambaya na ga silifas dinsa da butarsa a gefe babandaki ya zaga ba. Ga wannan furarsa gefesauran wacce ta dama masa yasha ya rage. Nan danan taga su iya salmai sun fito daga cikin gida suna rusa kuka idonsu yayi jawur suna riketa suna cewasannu hanna wannan ke aka yiwa mutuwa allah yajikan mahaifinki da sunanki a bakinsa har ya mutu.sai wani jiri ta kwashi hanna ta fada kanshimfidarsa ta rirrike filonsa ta kudindine ta runtseido ji take dama kasa ta bude ta fada da ita bakin cikin rayuwa ya isheta. Ta kwalla kara tana karacewa'' innalillahi waina ilaihi raju'un allah kanasane dani, allah ka san halin dana ke ciki. Allahbaka tsaneniba, baka kuma manta dani ba. Bani dakowa a duniya, babu wanda ya ragemin kumaallah kaine gatana kai ka halicceni, ka halicci mahaifina kuma ka halicci haisam. Ka hadani dasumuka saba kuma kai ka raba ni dasu allah. Allahkaine abun godiya. Allah na gode maka. Allahkaine jagorana, allah kar ka barni na dauwama acikin bakin ciki. Allahu akbar sai kowa ya rushe dakuka. Hatta iya abu data tsani hanna yau hanna ta bata tausayi matuka. Sai ta rushe da kuka ta dingarike hanna.....Muhadu 2 dancigaban labarin GANGARJIKINSA NA AURA 2 Part 1 Posted by ANaM Dorayi on 02:56 PM, 30-Apr-15 Under: Gangarjikinsa ta Aura Hatta iya abu data tsani hanna yau hanna ta batatausayi matuka sai ta rushe da kuka ta dinga rikehanna tana lallashinta. Da kyar matan nan suka iyabanbare hanna daga kan shimfidar mahaifintasuka shiga da ita cikin gida. Hanna tana rusa kukakamar rabta zai fita amma ta nemi hawaye ta rasa. Sai tayi shiru ta shiga dakinta ta kwanta ita damahaliccinta ne kadai tasan me takeji a ranta waniabune ya tokare mata zuciya kamar dutse abun yafikarfin kuka. Hanna ta kalli gabas da yamma kududa arewa taga babu wani mai fitar da ita dagatsananin bakin ciki nan da take ciki sai allah . Ta tuno nasihohin da haisam yayi mata aranarkarshen da ya rakasu tasha sai tasa hannu ajakarta ta lalubo carbi ta fara ja. Addu'oi iri iri hannako magana ta daina yi, yan gaisuwa a jere a jeresuna shigowa dakinta suna yi mata gaisuwa sai daikawai ta bisu da kallo har sha.awa take idan taga masu kuka da hawaye. Don ita kukan ma takenema ido rufe tayi ko taji sanyi a ranta ta kasa sallace kawai take fito da hanna tsakar gida sai kumaasuba take shiga bandaki tayi wanka.Banda wannan babu abinda hanna take yi sailazumi. Babu ci ba sha sai da aka ga kwana da kwanaki hanna taki cin abinci sannan su iya salmaisuke dama dan farau farau suka tsaya tsayin dakaakanta suka ce sai tasha kurba kawai take badondadi ba ji take kamar madaci suka dura mata donrashin jin dadin bakinta da take ji anyi sadakarbakwai kowa ya watse gida ya zama daga hannah sai iya abu . Yayanta ma suk sunyi aure kowacce takomagidan mijinta sai mutuwa ta dawowa hannasabuwa fil sai a yanzu ne ta fara samun zubar dahawaye . Kullum hanna kuka take rusa ita kadai adaki babu mai lallashinta kaico hanna. Sati daya satibayu iya abu ta gaji da ciyar da hanna, ayau da sassafe shida da rabi iya abu tazo ta fara bugawahanna kofa kamar zata karya kyauren hanna nakishingide akan abun salla tun asuba bayan tayisalla ta zauna jan carbi gyangyadi ya dauketakamar a mafarki take jin bugun kofar tayi firgigit tabude ido taga ba mafarki take yiba ta zabura da sauri taje ta bude kofar. Iya abu ta gani a tsaye takama tsantsan tayi kalar rashin mutunci. Hanna tajigabanta ya yanke ya fadi tasan rashin mutuncin yamotsa yau kuma sai yadda allah yayi da ita.tace'' hanna a to an gaba hada hadar mutuwa nayina allah nayi na annabi na ciyar dake a aljihuna har sati bayu. Ga rogo can n aika a siyomin zan dafa infara zuwa kasuwa ina siyarwa don nima dan kudincefanen hannuna ya kare ubanki bakar dawakadai ya bar mana a rumbu don haka ke kincikashinki saura ta zama kashin 'ya'yana zan ringasiyar da rogo ina samun na cefane ina tuka dawata, daga yau ki fara ziyar da kanki kafin a raba gadogama sunce sai na fita takaba kar kice daman bangaya miki ba dan kar in ajiye tuwan dumame nekizo ki gutsira mun tuwo in kuwa kika sake kikagutsirar mun sai na shakeki sai kin amayo shi.Hanna ta sunkuyar da kai kasa hawaye ya zubo shar tace'' to naji'' iya abu ta tafi ta barta anan atsaye kamar an kafata ta rasa mafita kuma. Hanna ta kasance tana kwana da yunwa sai ruwada take dirka wai ko iya abu taji tausayinta ta dingabata dan tuwo amma taga makatau, sai ta shirya tanufi gidan malam uba kanin mahaifinta ta shaidanasa cewar yanzu bata da abunda zata ci ko zaiajiye mata kwano a gidansa ta dinga zuwa tana daukar abinci ko da sau daya ne a rana ? Yanabudar bakinsa sai yace mata daman ta girma ta rikawai ita yar boko ga irinta nan abincin da zata ci yagagareta shi dai shawara daya da yaga ta dacetunda duk samarin garin suna tsoron zuwawajenta suce suna sonta ganin ita 'yar boko ce to ta yarda yayi wa alhaji bilya mai kudin garin nanmagana yazo ya aureta, zata fi karfin abinci don hartuwan shinkafa dafawa akeyi a gidansa dadaddare. Wani daci ya disu a zucitar hanna da tajibayanin kanin mahaifinta. Alhaji bilya da yakemagana wani shirgegen tsohon mutum ne matan sa uku yaya kuwa sun doshi talatin da yawaiyayensu basa gidan kuma jikokinsa ma sa'annintane, manomine ba laifi yana samu a dai garin shi maikudi ne amma ai tana zuwa gidan ada wajenkawayenta tasan yadda yanayin gidan . Watakatuwar tukunya ake dorawa a gidan kamar ta yan makaranta girki ma kadai ya ishi matan baya gadukan mata da yake yi yana da ciwon kuturtakuma harma ta fara fitowa hannunsa da bakinsazaka kalla kasan kuturu ne yatsun ne kawai basugama guntulewa ba amma sun fara diwa. Hanna tatabbatar lallai baba uba ba sonta yake yiba tunda zai hadata da alh bilya aure. Tayi shiru a durkushe agaban malam uba tana jin bayanan da yake matayace'' kin amince inje in sanar masa ko kuma kinada magana kiyi.Hanna ta nisa ta sunkuyar da kai kasa tace'' bababana kin jin maganarka bane ko naki yarda alh bilya fa kasan halinda yake ciki yana da lalurarkuturta. Baba yanzu zaka yarda in aureshi a haka?Malam uba ya fusata ya zabura hanna da fada'' kekinfi sauran matan zane ne, asirinsu a rufe ko goyashi zaki yi kina yawo dashi? Kuma shi da kansa yasameni yace yana sonki zai aureki. Nake jira daman a gama zaman makokin nan in shaida miki. Tundakinki sai ki tafi ki nemo abinda zaki dinga ciigardiya dake kinki aure babu mai ciyar dake, tashiki tafi bani waje mutuniyar banza. Hanna ta tashisumi sumi ta fice tana sharba hawaye. Tana fita tanufi makarantar boko, ta kuwa ci sa'a ta sami alhaji wani ma'aikacin da yake zuwa daga local gov'nt tarubuta takardar neman aiki[application]tun tuni zainemar mata aikin koyarwa a primary garin.Hanna cike da fara'a da murna tazo ta duekusahar kasa ta gaishe da alhaji ya amsa. Tun ma kafintace masa komai yace''hanna na kai takardarneman aikinki wajen manyana alhamdulillahkansilan garin nan ya gani ta sa hannu an kaiofishin sacretary'' murna ta rufe hanna yaci gaba da cewa'' to amma abunda sakatare yace shine bazasu iya daukarki aiki ba saboda akwai wadatattunmalamai a wannan makaranta akwai daimakarantun da aka rurrubuta za'a kara ma'aikataamma daman banda garin nan don haka sai daikiyi hakuri. Hanna taji ba dadi hankalinta ya tashi tace'' yanzu malam alhaji ko share share baza adauke ni ba ko a can local govnt din? Ya ce shareshare ai kinfi karfin yin shara hanna kije dai kicigaba da addu'a , na manta ma ban fada miki ba natambaya ance result dinku na jarabawa yafito amma an rike na f.g.g.c kazaure saboda kunyi matukar ci sosai wai har da masu nine distinctionkinga dole aki sakin sakamakon sai anyikyakykyawan bincike anga ko an baku amsa ne.Hanna tace'' binciken zai dadae ne? Ya ce''gaskiyairn wannan yana daukar kusan shekara ma ba'asaki ba. Amma daman da da result dinki a hannu da tuni na samar miki aiki ko ba'a garin nan ba.Hanna ta dade a tsugunne a gaban alhaji tayi shiruta rasa yadda zata yi can ta yunkura zata mikedakyar saboda jikinta yayi sanyi sai alhaji ya mikomata yan kudi yace'' gashi kya dan kashe'' dadi yalullubeta ta sami na cin abinci don yunwa take ji. Tayi masa godiya ta nufi gidan iya salmai . Ta isketaa zaure ta kasa zogale tana zaune tana jiran masusaya hanna tayi sallama ta shiga, bayan sun gaisaiya salmai ta ce'' hanna lafiyar ki kalau kuwa kinburkice gaba daya kamar ba keba? Hanna tayimurmushin karfin hali ta ce''iya yunwa nake ji ko da sauran dumame'' tace''wada na ajiyewa ya tafokwallo, rabonki ne zuba kici, da sauri hanna tamike ta nufi kicin don ta zubo tuwan. Iya salmai tabita da kallo, cike da tausayinta. Sharkab tana kukahanna ta fito ya sami iya salmai tana cewa allahsarki habu ka mutu kanar yarinya marainiya a duniya kaine daman gatanta'' hanna ta zauna asanyaye tana cin tuwan su duka hawaye suke yi.Iya salmai na tausayinta itama hanna na tausayinkanta. Bayan taci ta koshi tasha ruwa taje ta ajiyekwanon a cikin gida ta wanke hannunta sannantazo ta zauna ta shaidawa iya salmai halin da take ciki ta ce kuma tana neman alfarma idan da hali iyasalmai ta ajiye mata kwanan tuwo a gidanta tanaaika mata iya salmai taji dadi kwarai da hanna batayi kauron baki ba tazo ta sanar mata da wuri taceinsha . Allahu kome taci da kashin hanna to ammaitama ba kullum suke dora tukunya sau uku a rana ba.Itama ba da ko ta agareta ba bishiyoyin zogalene burjik a shuke a gidanta. Ta tsinka ta dafa tasayar ko azo a tsinka a danye a biyata. Daga ita saiwada wani dan kanwarta data rasu ta barshi tunranar da aka haifeshi ta dauke shi. Shima yanakokari ya samo kudi, to da haka suke cin abincin, ranar da ba'a samu ba su sayi na siyarwa ko suhakura idan babu kudin sayan na sayarwa. Iyasalmai tace'' ai idan naga 'ya'yan Habu raina dadiyake yi, ba don habu yana dan uwana bamasoyayyar da nake yi masa ce Hanna har yau ina jindandanonta a raina'' hanna tayi shiru tana tunani a ranta tana kuma tausayawa kanta cewar'' in har iyaSalmai bata daina jin dandanin soyayyar da takeyiwa mahaifinta ba har yanzu shekararsu tafiashirin da biyar da rabuwa gashi kuma ma har yamutu rana zancen sonsa ashe har abada iya Salmaibaza ta daina jin dandanon son nanba. To itama tana kyautata zaton haka zata kasance da donHaisam tunda gashi dai yanzu bata ganinsa yayiaurensa ma amma sai kara jin tana kara sonsa takeashe itama haka zata dauwama kenan har karshenrayuwarta. Soyayya gaskiya ce'' Hanna ta fadaabaiyane. Iya salmai tace'' soyayya gaskiya ce Hanna. Haka dai suka yini suna hira hanna ce tadafa musu abincin dare suka ci sannan suka yisallama Hanna ta tafi gida. Sun rabu akan iya Salmaizata ringa turo wada yana kawo mata abinci duksanda suka sami damar dafawa. Haka hanna ta kasance duk sanda iya salmai tadafa abinci ta aiko mata taci ranar da itama batadafa ba haka hanna take zama da yunwa. Ta ramekurkut da ita sai ido da dogon hanci tayi duhukuma saboda tsaban wahala da tsananin tunani .Ranar da iya abu ta fita takaba sai maigari ya hado malaman garin da masu fada aji na garin da yanuwan malam Habu don raba gadonsa ga iyalansa.A zauren gidan aka zazzauna ga iya abu gayayanta kakaf mata da maza ga hanna a gefe.Itama da iya salmai. Maigari yace'' a karantawamamacin kulhuwallahu kafa uku uku, da inna a'adaina kalkausar uku uku aka shafa Allah yakaikabarinsa. Sai maigari ya fara da cewa'' malamHabu ya rasu yabar mace daya da yaya takwas.Dukiyarsa kuwa wannan gidan ne da kumakatuwar gona. Amma tun ranar daya mutu akabiya masa basussuka da ake binsa da dan kudin daya bari. Ga manyan malamai nan zasu raba gado.Ga sunayen 'yayan nan a wajensu zasu shiga cikingidan su tsatstsaga su bawa kowa nasa bangaren.Iya abu ta nisa tace ina da magana nidai nicematarsa uwar yayansa kuma bare daya ce Hannedon haka a tabbata an bata bangarenta daban kar a saka min ita cikin kason 'yayana azo ana rigima.Maigari yace'' ai abu rabon gado ba'a cewa bareAllah ne ya raba da kansa don haka duk yadda takama haka za'ayi. Malamai sun yi iya kokarinsu sunkacaccala dan mitsitsin gidan nan d gona. Allahcikin ikonsa hanna bata tashi da komai ba sai rumbun ajiyar abinci,wani dam mitsitsine kasace turmus a kasan da gidan tururuwa sai dan wanibangare karami a tsakar gida shine kashin hanna agona kuwa bata ciki. Murna ta lullube iya abu gonada gaba daya dakunan gidan nata ne da yayanta sai tace'' wannan rabo yayi daidai to yanzu ta tashidaga dakin nan'' mai gari yace haba abu har yanzutsangwamar da kike yiwa hanne baki bari ba harmahaifinta ya mutu bakya rangwama mata ba''iyaabu tace a'a babu wani rangwame yan haya zansaa sauran dakunan ina karbar kudi wannan abu ne fa na gado. Nan fa duk suka hadu suna ta bawa iyaAbu hakuri ta barHanna taci gaba da zama a dakinda take har Allah ya yanke mata wannan zamatunda komai dadewa aure zata yi. Iya Abu takekashe idanuwanta ta ce in anga ta yadda Hannayauta sake kwana cikin dakin nan nata to ta bata kudin haya ne a matsayin tana haya.A cikin mutanen dake wajen harda Alh bilya ya ceto tunda Abu tace haka shi yayi alkawari zai dingabiyawa Hanne kudin haya daga yau ya tambayiAbu ko nawa ne kudin hayar dakin da hanne keciki ta kai kaice ta zambada kudi ya zaro ya biya ba tare da ya nemi ragi ba, ya biya na shekara ya saniya abu kora da hali take yiwa Hanne ta zambadakudi dan ace yayi tsada a kama mata a wani gidacikin ikon Allah sai taga ya biya.Mai gari da sauran mutanen dake wajen suka dingashiwa Alh bilya albarka, Hanne ita da baba Uba ne kadai suka san manufar Alh Bilya shi a nufinsaauren hanna zaiyi shi yasa ya fara mata hidima,wani gululun bakin ciki ne ya dira a zuciyar Hannamusamman da ya biya mata kudin haya ta san lallaida gaske yake auren nata yake so yayi ita ko garaa kasheta da a daura mata aure da wannan mutumin kamar tace bata son kudin hayar baza tazauna a gidan ba karya biya sai tayi tunanin in bagidan uban nata ba a ina zata zauna saita hakurakawai tayi shiru idan tace zata koma gidan iyaSalmai to ai daki daya ne kacal a gidan dan karamiita da wada suke kwana a dakin ba zaiyu ita ta hadu da Wada a daki daya ba saboda yanzu Wadashekararsa goma sha takwas yama girme ta dashekara daya don haka ya haramta su cusu a dakidaya bayan nan babu gidan wanda zata iya zuwata zauna duk danginta.Da daddare bayan kowa ya shige bacci ya kwanta hanna na juyi a yar katifar ta kasa bacci tsananinbakin ciki ne ya dameta a ranta bau abinda takenanatawa a ranta sai zancen hayar na. Ita da gidanubanta yau ta zama 'yar haya sai ta rushe da kukahar ta gaji. Tace''Allah kana ji, kuma kana ganina,kana kuma sane da irin abubuwan bakin cikin da nake gani tun ranar da mahaifiyata ta sakoni aduniya Allah ka fitar dani. Kaine gatana ya sarkinsarakuna. A haka Hanna ta kasance har shekaraguda da rasuwar mahaifinta. Yau taci abinci gobe tarasa wannan bai dameta ba sosai irin zurga zurgarda Alh Bilya yake yi a danginta yana cewa shifa yana so ya aureta. Dan har yaje ya sanarwa damaigari. Maigari yasa aka kira Hanna fada ya shaidamata abunda Alh Bilya yake nema a wajenta shin taamince zata aureshi, ta yarda tana so a dauraauren ? Hanna ta fito gar da gar ta fadi gaskiyatace'' ranka ya dade banki jin shawarar da ka bani ba amma dan Allah ina so a barni haka bana so inauri kowa. Gaba daya aka dau salati aka fara yiwaHanna ''cari to ba'a garin nan ba. Duk garin nanwacece ta taba kaiwa shekara goma sha takwas baa yi mata auren fari ba? Hanna tace'' ba zan iyaauren Alh Bilya ba a matsayinsa na mahaifina dan ni tamkar mahaifi yake a wajena. To haka akayi daHanna a fada. Alh bilya yaji haushin Hanna data kiyarda amma yasan tuggun da zai tafka mata yarama.Bayan anyi haka da hanna a fadar maigari dakwana uku. Alh bilya yazo har cikin gidan su hanna da rana tsaka . Hanna na daki a kwance tanajin yunwa tana jiran a kawo mata abinci daga gidaniya salmai tana fargabar ko suma basu yi abincin bane yau sai ta jiyo muryar alh bilya yana rafsasallama iya abu ta fito iya abu tace''yau alhaji dakanka a gidan namu. Yace'' eh wallahi zuwa nayi mu gaisa inji ko yaushe kudin hayar dana biyayake karewa? Iya abu tayi dariya ta sosakwarkwata a kai tace'' ai sauran wata uku ne inajin''ya ce''to ki raba kudin hayar gida hudu ki daukikashi uku naki ki bani kashi daya ragowarwatannin uku ki kori hanne daga dakin da take haya in bata biya ki ba ba ruwana'' iya abu ta batarai tace. To ni yanzu na kashe kudi yaya kake sonayi a ina zan samo kudinka da zan dawo makadashi ? Hanne fakara'u ko sisi bata dashi ina zayasamo wani kudin haya ta biyani? Gaskiya alh bilyakai ya dace kaci gaba da biyan kudin haya don haka kace a gaban maigari''yace''kash ni bakifahimceniba abu ba don in takura miki ba nace kibani sauran kudi ji rike sauran kudin ina nufinyanzun ki koro hanne daga dakin da take donnibada yawuna take zaune a dakin ba kuma ba'akudina ba. Iya abu tayi dariya tace''oh na gane wato yanzu dai in rike ragowar kudin watanniukun da suka rage kenan sannan in koro hannewaje idan bata biyani kudin haya ba ko. Ko bahaka kake nufi ba? Alh bilya yayi dariya yace''hakanake nufi mana.iya abu tace an gama ai a gabankazan koro shegiyar. Gaban hanna ya yanke ya fadi tayi zumbur ta tashi zaune ta dafe kirji tana tainnalillahi wa'inna ilaihirraju'un. Iya abu ta wangalelabulen dakin ta shiga budik ta sami hanna a kankatifa a zaune ta mikawa hanna hannu tace''banikudi. Hanna tace''bani da kudi. Iya abu ta wawurijakar hanna zata wurgar waje hanna ta rike tana mata magita tayi hakuri dan Allah ta rufa mata asiri,amma kamar zuga iya Abu take.Hanna ta fito da gudu daga dakin ta zo ta durkusaa gaban Alh Bilya tana rokonsa dan Allah yayihakuri ya bar mata kudin hayar wata uku kafin nanzatasan yadda zatayi ta sake biya. Amma yayikunne uwar shegu da ita yana cewa''yauwa Abu ki tattaro kakaf kayanta ki watso''ana cikin wannanhali sai ga Wada nan dauke da kwanan abinci yakawowa Hanna abincin rana ya sami Hanna kacekace tana kuka a durkushe a gaban Alh Bilya tanarokonsa iya Abu kuwa tana ta faman watsi dakayanta. Cikin kuka Hanna tace'' wada kaga halin da nake ciki jeka ka kira iya Salmai tazo ta rokarsu.Nan da nan wada ya garzaya dan ya shaidawa iyaSalmai halinda yazo ya tarar da Hanna. Bayantafiyar wada ba dadewa sai ga iya salmai da maigarida tawagarsa sun shigo gidan suka iske hanna acikin wannan hali. Maigari ya ce'' subhanallai Alh Bilya da girmanka meye haka? Alh Bilya yace''ranka ya dade babu yadda za'ayi taci gaba da zamaa cikin kudina bayan bata sona shi yasa nazo na ceto in Abu taga zata bar Hanna taci gaba da zama akyauta to. Amma ba dai nine ke biyan kudin nandole Hanne ta fita don bazan barta taci gaba da zama a kudina ba tunda bata sona. Nan dai akahau bawa Alh Bilya da iya Abu baki ana musuwa'azi da nasihohi akan rayuwa ce kuma sumasuna da yaya zasu iya mutuwa su bar yayansusuma ayi musu haka. Hanna tasa gefen zaninta tagoge hawaye ta mike daga durkusan da take yi ta juya ta kalli su maigari tace'' ku kyalesu ni nahakura da zama a dakin zan koma rumbun inzauna hanna ta fara dibar jakunkunan ta tanashigarwa cikin rumbun nan mai gidan tururuwa dacinnaka ga bunhunhunan dawa da kaikayi.....ANA CIKIN WANNAN hali ne Musa danmakwabtansu ne ya shigo yace'' wasu maza gudabiyu gasu nan a waje wasu farare ne kamarlarabawa sunce suna neman Hanne 'yar gidanMalam Habu. Mai gari yace'' larabawa daga ina ?Musa yace sunce daga Niger suke maigari yace'' to muma ai tafiya zamu yi mu tafi kawai, har Hannasuka yiyo waje wasu samari farare sol sol ne gudabiyu a tsaye a kofar gidan daya daga gani kotambaya babu jinin hanna ne don kamar su dayakamar an tsaga kara maigari yace ''kune bakindaga Niger ? Suka amsa 'eh' sannan suka duka suka gaishe dasu maigari. Hanna ta tsaya a gefetana kallon wadan baki nata bata san suba ammadaya daga cikin samarin kamarsu daya futik dagagani babu tambaya daga tsatso daya suka fito.Maigari yace'' to ga Hanna . Yaya kaman baku sanjuna ba. Mai kama da Hanna yace'' ni sunana Ahmad wannan abokina ne sunansa Bello Madu. Nikanin mahaifiyar hanna ne uwa daya uba daya.Hanne bata taba ganina ba ban taba ganinta bashine nazo na nemota don muga juna'' Hanna najinhaka sai ta daka tsalle ta rungume Ahmad sai itadashi suka rushe da kuka. sai suka rushe da kuka. Maigari da sauran mutane sai suka hau girgiza kaisuna masu tausayinsu. Maigari yace'' Alhamdulillahgara da Allah ya kawo ku sai mu koma daga cikin atattauna. Bayan kowa ya sami waje ya zauna,Hanna ta tashi ta dauki kwano ta kwalfo musuruwan sha a randa ta kawo musu, bayan sun sha. Maigari ya fara bayani ya shaida musu duk halindaHanna take ciki yanzu ma ga jakunkunanta nan awatse a waje dakin da zata zauna ma yanzu yazama garari. Ahmad ya matse hawaye yace'' hakikatuntuni munji irin halin da mahaifiyarki ta shiga harta rasu mun san kuma halin da yarta Hanne zata shiga amma da yake ni ina yaro bani da ikon inzoin dauketa shi yasa na hakura akwanakin nankuma na dinga mafarki iri iri na 'yar uwatamarigayiya uwar Hanne. Kullum na kwanta baccisai inga yayata Habi tazo tana cewa Ahmad danuwana yanzu baza kaje ka nemo 'yata ba Hanne kaga halin da take ciki ba a duniya ba, ko darenjiya ma nayi mafarkinta abu daya kuma takemaimaitawa don haka yanzu daman nazo da niyyarmu tafi da ita ko da mahaifinta yana nan zanrokeshi ya bani ita idan batayi aure ba in tafi da ita.Balle kuma yanzu da ya rasu dole in tafi da ita. Iya abu ta tabe baki tace malam tunda ransa ya hanaakai hanna wannan garin'' maigari da jama'arsa suka yiwa abu caa suka rufetadafada suna cewa'' ba yanzu kika gama mata watsida kaya ba? Bayan bakar wahala da take sha tuntana karama ta zamo tamkar baiwa a gidannan.Ahmad ya ce'' ba saikun bata bakinku bama wajenbata amsa mu dai zamu tafi da ita . Sai yanzu daya mutumin yayi magana wato Bello Madu yace'' aianan kusa muke a garin dashi muke. Dashi dababban mutum ai border ce ta raba. Ni costom neina aiki a border lokaci lokaci zan dinga kawomuku Hanne kuna gaisawa. Ahmed ya katse shiyace ''duk zancen ka lallashi matan nan bai taso ba kaga kankat din gari wato maigari da jama'arsasun bamu izinin mu tafi da ita to wacece kuma zatace sai hanne ta zauna yunwa ta kashe ta. Iya Abutaji wani dacin bakin ciki ya rufeta ganin Hanna tasami wajen da zata je ta huta. Taso ace da ta yiwaHanna watsi da kaya duk garin ta rasa inda zata zauna. A haka dai aka rabu Ahmad da abokinsaBello Madu suka yiwa mai gari da jama'arsa sallamasuka daukarwa Hanna jakunkunanta, Hanna tayafa gyalenta tarungume iya salmai suna kukanrabuwa Hanna da kawunta suka tafi.sun isa garin Dashi da daddare gidan Ahmadsuka sauka. Ahmad yana da mata daya da 'ya'yabiyu , sunan matarsa Hajir itama irinsu ce buzuwa.Hajir ta tari hanna cikin fara'a da murna ta kaitadaki ta kawo mata ruwa ta sha sannan ta zaunasuka gaggaisa sannan taje ta shirgowa hanna tuwo. Hanna taci tuwo nan tamkar tunda allah yahalicceta bata taba cin tuwo mai dadin haka basaboda tsabar yunwa da take ji, taci tayi nat sannantace a nuna mata bandaki zata yi alwala Hajir tanuna mata. Hanna ta shiga ta dauro alwala tazo tayisalloli tana idarwa taje ta watsa ruwa tayi wanka ta kwanta. Hajir taji tana son Hanna, tana sonta dakawa daga gani ma sa'an nune, hajir ta zauna agefen shinfidar Hanna na kwance suna ta hira kalakala,Hajir bata bar dakin ba sai da taga Hanna tafara bacci sannan ta hure mata fitila ta rufo kofa tafita ta nufi dakin kwanciyarsu. Da asuba Hanna ta farka taji ana kiran assalatu ta mike ta nufi ban dakitayi alwalla tazo tayi salla ta zauna tana Lazumi.Gyangyadi ne ya dinga daukar hanna ta mike takoma kan katifa ta koma bacci tayi ta barci har shadayan rana babu wanda ya tashi Hanna sai da tayibarcinta ta gaji ta farka dan kanta. Tana tashi tayi ido hudu da soye soyen abinci kala kala Hajir tazota jera mata. Ba Hajir kawai ba 'yar uwan uwarHanna fa yawa labari yakai musu cewar hanna tazodon haka suka aiko mata da abincin karin kumalloiri iri sunka ce kafin suzo su ganta. Hanna ta fadawanka tayi brush sannan ta saka kayanta tazo ta zauna a gaban abincin burjik a jere a tsakar dakintaduk nata ne sai taji wani farin ciki ya lullubeta ba'asabanba, yau hanna ce da barcin safe ta farka tagaabinci burjik an jere mata haka Allah yake, duniyajuyi juyi. Tun kafin hanna ta gama karin kumallo tajitsofaffi da mata suna sallama a tsakar gida, yan uwan mahaifiyarta hanna ne suka fara cinci rindonzuwa ganin hanna, sai koke koke daga su harHanna taga dangin uwarta cunkus amma suka cemata wadannan ma kadan ta gani don tushenzuri'arsu Azbinawa ne [buzaye] suna Agadas state .Sai dai wani abu guda da hanna ta lura duk danginta talakawane sosai suna cikin rashi wasuNono suke sayarwa rugage suke wasu kumamanoma ne. kawu Ahmad ne kawai dan Bokowayayye mai dan hali akan sauran koyarwa yake amakarantar firamaren garin har ya sami matsayinmataimakin headmaster. Shima dai rufin asiri ne kawai ba wani arziki gare shiba. Gidansa ginin kasane dakuna uku ne, bandaki da zana aka zagayekicin kuwa a tsakar gida aka dasa murhuna. Hakadai Hanna taji ta shiga wata sabuwar rayuwa maidadi fiye da rayuwarta da agidansu. A koda yausheyana godewa Allah da yayi mata canji daga ukuba da bakin ciki hantara ya kawo ta inda aketarairayarta. Hanna da Hajir sun shaku sosai a kodayaushe suna tare suna hira wasa da dariya. Tunhanna na boyewa hajir wasu abubuwa nadangane da rayuwarta har ta yaba da hankalinta tafara gaya mata wasu abubuwa da suka faru da ita ada na dangane da tsananin son Haisam ranarrabuwarsu. Tace har yau kullum da daddare sai tayikuka idan taje kwanciya barci saboda tunaninsa.Hajir ta tausayawa hanna sosai har hawaye tayimata ,daga karshe tayiwa hanna nasihoho akantayi hakuri kaddara ce daga Allah haka Allah ya rubuto musu.BAYAN zuwan hanna da kamar wata guda kawuAhmad da sauran manyan danginsu suka kiraHanna babban zauren dake gidan. Bayan ta gaisheda kowannensu ta koma gefe ta takure. BabaSha'aibu yace'' Hanna kinsan dalilin da yasa mukakira ki nan? Hanna cikin ladabi ta amsa musu a'a yace to a matsayinmu na iyayenki da kakanninkimunyi nazari mun kuma tsayar da shawara abindanake nufi da munyi nazari shine bai kamata ba muzuba miki idanu haka nan ba babu aure don hakaya kamata kiyi aure a watannan kuma. Gabanta yayanke ya fadi ras dajin kalmar aure cikin rudani tace''....... Wazan aura ai ni bani da kowa a garinmuanan garin ma babu wanda yace yana sona.'' suduka suka kyalkyale da dariya. Ahmad yace''hanna kwantar da hankalinki dole mu aurar dakega mai sonki kece dai baki sani ba amma zuwankigarinnan maza sun doshi goma suka sameni suka ce suna sonki shawarar da muka yanke ita cemuduba a cikin waye yafi hankali. Addini. Sana'aasali wanda zai rikeki tsakani da Allah mu aura mikishi tunda ke bakuwa ce ba sanin halayensu kika yiba babu kuma isasshen lokaci da za'a barki kinasoyayya dasu har ki zabi miji mu baza mu zaba miki wanda zai cucekiba . Hanna babu wanda ya fadomata a rai sai Haisam, soyayyar da take yiwa Haisamsai kara yabanya take a cikin ranta, Hanna ta ciresha'awar auren wani a rayuwarta tunda ta rasaHaisam shine ma hawaye yake zuba dagaidanuwanta don tasan ta rasa wanda take so duk duniyar nan ta rasa farin cikin kuma. Wannanhawaye na hanna da yake zubowa dagaidanuwanta yasa jikinsu ahmed yayi sani kumamamaki ya rufe su yaya za'ayi hanna ta fara kukatun kafin taji waye aka zabar mata ta aura. Koakwai wanda ta kudira zata aura ne basu sani ba ? Inna rabi tace'' Hanna kukan me kike bafa cewamuka yi dole sai kin auri wannan da muka zabarmiki ba idan kina da wanda kike so fadi mu auramiki,daman ganin babu kowa ne shi yasa muketunanin hadaki da wani. Hanna ta share hawaye tagirgiza kai tace'' babu wanda nake so zan aura dukwanda kuka zabar min zanyi biyayya in aure shi kowaye kuma. Nasan baza ku zabar min wanda zaicutar dani ba'' gaba daya suka fara shiwa hanna albarka suna jinjina mata bisa tsananin biyayya datake yi musu allah yayi mata albarka. Kawu ahmadyayi gyaran murya ya gyara zama yace'' hanna tunfarkon zuwanki abokinna koma ince ya zama danuwana saboda tun muna yara muke tare nasanhalinsa ciki da bai fiye da uwar data haifeshi bata sanshi ba fiye da yadda nasan yadda yake yana damutunci da sanin ya kamata yace yana sonkitsakani da allah zai aureki wannan aboki nawashine bello madu abokina din nan da mukajenigeria garinku dashi muka daukoki . Yana dasana'arsa kuma yana da ilmi gaba daya boko da arabiya yanzu ma babba ne ba laifi a aikinsa aikincostom yake sune suke tsaye a bordar nigeriazuwa niger. Ni dai a ganina bello masu ne kawai yacancanci ya aure ki ko ya kika gani? Iya ma'idatace'' wanne irin yaya ta gani bayan ta gamamagana tace ko waye muka zabar mata tana so. Cancanta ma ai ba sai an fada ba sun dace ai''hanna ta sukuyar dakai kasa sai hawaye shar yasake keto mata. Bello madu kam ya cancanci asoshi bashi da makusa kyau kuwa kamar shi yayikansa dan buzaye asali kamar balarabe, hankali datausayi kuwa ba'a magana don da yaji labarin hanna hawaye ya dinga yi don tausayinta bashi damakusa ko kadan amma ita abun da ya kara satakuka shine tana matukar ganin mutuncinsa donhaka bata so aka ce shine zai aure taba don dukwanda ya aureta sai yayi hakuri sabod bazai samisoyayyar taba GANGAR HIKINTA zai aura zuciyarta na wajen haisam har abada, hankalin hanna yasake tashi sosao da taji sunan wanda zata aurakawu ahmad yace'' ni wannan kukan naki ne yaketsoratani hanna kiyi magana idan akwai wani abunda yake damunki. Hanna tayi dan murmushi tagirgiza kai ta ce'' babu kimai zabin da kuka yi min yayi. Inna goshi ta dau buda kiwa ya hau cewa''allah ya sanya alheri ya baku zaman lafiya. Hanna tamike ta shiga cikin gida bata tsaya a ko!ina ba sai adakinta ta rufe kofa ta fada kan katifa sai ta budesabon shafin kuka mai tsanani taji a ranta kamarwata sabuwar soyayyar haisam aka kara zuba mata taji sonsa ya sake sartseta kamar zata yihauka. Bayan anyi haka da kwana uku hanna nazaune a tsakar gida tana tankaden gari da yammatana taya hajir aiki, hajir kuma na wajen murhutana kada miyar kuka, suna taba yar hira hajir tace''hanna ina ganin kinfi sauran mata sa'ar samun kintsatstsan miji a duk yan matan garin nan sabodaduk yawanci yan matan garin babu wacce batakaiwa bello madu hari ba farin jini gareshi sosai.Kyawunsa ne ko kuwa illminsa , ko kuma jan ajinsane yake rudarsu oho? Amma ke gashi kwatsam yadamu da sanki kinsan tun ba yauba kawunki ahmad ya fadamin cewar bello madu yana sonkiamma ya gargadeni da nayi shiru kar in sanar mikihar sai ya sanarwa da magabatansa shima. Hannata cije tayi dan murmushi tace'' hajir kenan watonayi sa'a sosai ashe dana sami bello madu ta sama.Ba tare dana wahala ba? Amma ni a wajena sai dai ma ince shine yayi sa'a sosai ma kuwa.Alhamdulillah amma akwai matsala tabbas. Hajir tajuyo gaba dayanta tana kallon hanna can tace'' bangane akwai matsala ba. Wacce irin matsala kumahanna ? Ko bakya sonsa ne? Hanna ta girgiza kaitace ta ce a'a ni naki shi bayan shine zabin iyayena ina sonsa mana. Muryar bello madu ce tace.''assalamu alaikum''.Kai tsaye ya shigo cikin gidan kamar yadda yasaba shigowa daman. Kai tsaye wajen hanna yadosa. Hajir ta amsa masa sallaman gami da yi masatsiya ta ce'' oh dan halak kaki ambato yanzuzancenka fa muke yi ango kasha kamshi dagazuwanka ka doshi wajen hanna da idan kazo wajen wa kake dosa? Bello madu ya kyalkyale dadariya yace'' kai hajir kin fiye tsokana kinsan da saiinyi sati biyu a boda ban damu da zuwa garin nanba amma yanzu kusan kullum sai nazo garin nanko banzo gidan nan ba ina jin dadin garin sabodamatar da nake so tana cikin garin. To yanzu an banu izini inzo wajenta kina nufin sai in doshiwajenki duhu bayan shigowata hasken fuskarhanna ne ya bugi idanuwana. Kinsan ko a kabarihaske ake nema ana neman tsari da duhu. Hajir tarike baki tace'' ah bello madu daina hadani daduhun kabari allah ya baka hakuri'' wannan hira tasu ta bawa hanna dariya bata san sanda tatuntsire da dariya ba duk da wani kululun bakinciki daya dira a ranta yanzun nan da bello madu yashigo haisam kawai zuciyarta take haska matainama inama aceda haisam za'ayi musu auren nanwata guda ya rage ayi bikinta. Bello madu yace'' hajir yi hakuri bada duhun kabari nake hada kibani na isa? Ai nasan kokarin da kike min wajenturani fadar zuciyar hanna tun dazu ina zaune atsaye ina jin hirar da kuke yi. Kuyi hakuri ba labe namuku ba ina doso kaina bello madu naji anaambato shiya sa na dakata sai dana gama jin komai'' hajir tayi dariya tace a'a baba bello ka faralabe a gidan mutane dai kawai zaka ce min'' yakarasa wajen hanna ya jawo wata kujera a gefentaya zauna a hankali yayin daya kafawa hanna idoyana kallonta. Ji yake tamkar ya hadiyeta sabodason da yake yi mata. Fargabarsa daya yana tsoro kada hanna taki amincewa da soyayyar da yake yimata haka nan bayan abokinsa ahmad ya shaidamasa an bashi hanna yayi farin ciki amma farincikin ragagge ne yana gudun kada a takurawahanna ta aureshi yazo ya rasa soyayyarta ammayau sai gashi da kunnensa yaji hanna tace''ni na kishi bayan zabin iyayena ina sonsa'' don haka yauyafi kowa farin ciki. Hanna ta dago a kunya cetagaishe shi ya amsa cike da fara'a ya mika hannu yakarbi rariyar dake hannunra ya fara tankade. Hajirkuma tana yi masa tsiya tana cewa'' wai bellowannan bamu san wanne irin abu za'ayiwa hanna bayan anyi aure tuwan ma kai zaka dinga tukamata. Bello yace ke kin fadi kadan tauna abincikawai bazan yiwa hanna ba saboda bazaiyu intauna mata ba amma a baki zan dinga bata bayanna dafa mata domin hanna tafi saraunoyar da takemulkin duniyar nan idan ma akwai yadda nake jinta a raina,Ga mamakinsa sai suka ga hawaye shar yatsiyayo daga idanuwan hanna. Babu abinda ya satakuka sai tausayin kanta dana bello madu dominkowannensu son maso wani yake yi, inama haisamne yake jinta a ransa haka kamar yadda bello maduyake jinta a ransa. Shima ina ma yadda yake sonta tana sonsa haka'' allah sarki bello ka makara''hanna ta fada a ranta' sai bello ya kurawa hannaido kawai yana kallo sai ya juya ya kalli hajir wacceitama tayi kasake a tsaye tana kallonsu. Ya miketsaye ya kade garin da yake hannunsa yace dahanna ta taso suje zaure yana son ganinta yana da magana da ita. Hanna ta mike ta dauko ruwa tawanke hannayenta ta yafa gyalenta tana biye dashisuka fita zaure. Tambayoyom da bello madu yajerawa hanna sun doshi goma dom son yaji meyeya sata kuka ko aurensa ne bata so amma duk daa'a hanna take amsa masa. Domin idan ta kuskura ta bayyana abunda yake ranta ta sake shiga ukutasan bello ba zai takura yace sai ya aure ta bahakura zaiyi idan ya fasa aurenta wazata aurakuma tunda bata da maganin ciwon da yakedamunta. Na san na rasa haisam, na rasa shi kumahar abada na rasa soyayyarsa na rasa farin cikin rayuwata, meye ya rage mun a duniya kuma?Banda jiran ranar mutuwa. Bello ya katsewa hannatunani yace'' to tunda na tambayeki kince ba komaiakwai wata magana guda da nake son muyi dakehanna don allah kiyi hakuri ki sake yin hakuri daduk yadda kika tsinci rayuwarki, abinda nake nufi shine watakila hajir ta fada miki ina da gida nawana kaina yanzi ma a ciki nake zaune nan za'a kaikibayan anyi bikinmu, to kinsan halin iyayemusamman ma mata mahaifiyata ta kekashe kasatace lallai lallai sai dai a kaiki cikin gidanmu ma'anagidan da take zaune da kishiyarta wanda ba karamar takura bane dakine kwaya daya jal ganata ga wanda za'a kaiki. Kiyi hakuri ko bayanbikin zanci gaba da bata hakuri akan ta yarda inmaida ke gidana'' hanna ta sunkuyar dakai tacekawu wannan ba wani abu bane da zaka damukanka. Kaabi maganar mahaifiyarka domin abunda babba ya hango yaro koya bishiyar rimi bazai ganoba, ita ta haifeka tafika sanin dalilin dayasa tacemaka ka zauna da matarka a kusa da ita . Allah yabamu zaman lafiya gaba dayanmu ni da ita. Ni dakai kuma na gode'' wannan kalamai na hanna yakwantarwa da bello madu hankali don bai taba zaton hanna ba zata damu ba idan taji yare dasurukai zata zauna amma sai yaji ita take kokarin yimasa nasiha, akan ya kwantar da hankalinsa yabimaganar mahaifiyarsa. Kuma hanna ita ce take yimasa godiya. Daga karshe ya yiwa hanna sallamayace zai koma wajen aiki sai nan da kwana hudu zai dawo an turashi tsakanin boda dake tsakaninmaigatari da niger da zarar ya dawo za'a kawo lefeinsha allah. Hanna tayi masa fatan dawowa lafiya yatafi ita kuma ta shiga gida,Ta iske hajir tana kwasar tuwo . Taje kusa daita ta jawo kujera ta zauna. Hajir ta kalleta taceamarya a gidan custom bello madu kinsha kamshi,amaryar nan da wata guda. Wai ya naga duk jiknkiyayi sanyi ne har koke koke kike yi? Koda yakemuma fa duk munyi wannan don gabanin bikina kurket na rame sai kuka ina zaton auren waniabun tashin hankaline ashe babu abinda ya kai shikwanciyar hankali, ke kuwa daga ke sai masoyinkiku biyu a gida ku rakashe kowa kokarin yafarantawa dan uwansa yake yi. Ke gidanki nasiminti ne kewayayye ai bello madu ya zuba sumunti a gidansa tal a lailaye da simunti kamar abirnin. Mu da muke gidan kasa ma muke jin dadinrayuwarmu balle ke'' hanna ta ce'' kai hajir ai dagidan simintin dana kasar duk dayane yanzu yakecemun mahaifiyarsa ta tubure lallai lallai bata yardata kaini gidansa ba sai dai in zauna a gidansu. Hajir ta zabura ta wurgar da marar da take kwasar tuwota mike tsaye ta rike haba da hannu tace'' hanname kika ce kina nufin yanzu gidan su bello za'akaiki? Lallai mun shiga uku mu masu kai amaryama balle ke da zaki zauna da ita. Hanna ra jawohannun hajir ta zaunar da ita tace'' hajir zauna mana muyi magana daga zaune me yasa kika cemun shiga uku wani abune ? Hajir tayi ajiyar zuciyata koma ya ta zauna tace'' hanna bazan boye mikiba a gaskiya innar bello bata da haki saboda dukgarin nan babu wanda bai san bala'in inna hauleba har tafi iya abu matar babanki da kike bani labarinta don tun maigidanta yana nan bai rasu batake azabtar da kishiyarta indo wahalar duniyarnan yau idan kika je gidan indo da yayanta tamkarbayi ne a gidan. Debo ruwa ma a rafi ya ishekibayan zuwa gona da sassafe amma shi bello meyasa zai yi mana haka bayan yasa halin mahaifiyarsa ko da yake ba laifinsa bane don idanta saka musu kara basun isa su tsallake bamusamman bello yana yi mata ladabi sosai fiye dasauran kannanshi shine babba a gidan. Ina jin batsso yayi nisa da ita gani take komai ya samu yanzuke zai dinga dankawa gaba daya'' kafin hanna tace wani abu ahmed ne yayi sallama ya shigo sukaamsa masa gami dayi masa sannu da zuwa. Amurtuke ya amsa sannan ya juya ta kalli hajir tadaka mata tsawa yace. Ke hajir ki iya bakin kidanme kike kokarin rikita hanna akan aurenta dabello madu akanta aka fara zama da sirikai'' ya juya ya kalli hanna yace'' to saikin toshe kunnuwankishi aure dan hakuri ne kiji kiki ji ki gani kiki gani,ladabi da biyayya shi zai rabaki da masifa datakurawar surukarki. Kada ki yarda da 'yan zugamasu nuna miki kin hadu da masifar suruka mutumko shaidan ne yasan mai kyautata masa don haka idan kika bi inna haule sau da kafa dole ta dagamiki kafa. Bawai nace hajir tayi karya ba hakahalayyar inna haule take amma sai kinyi hakurikindaure kin mata biyayya zaki ga ashe duk abundaake fada maki ba haka take bama'' hanna tasunkuyar dakai kasa tace'' to kawu naji abunda ka fadamin zanyi amfani dashi na gode madalla'' tamike ta shiga daki. Ahmed ya juya ya kalli hajirwacce ta cika tayi fushi taf kamar zata fashe'' yashafa kumatunta yace'' ke kuma daga maganameye abun yin fushin'' hajir tace'' haba ahmed mekake nufi da ka ce kada hanna ta saurari yan zuga, kana nufin nice yar zugar kenan zan hanata yinaure ko? Ya ce a'a abunda naga laifinki shinemuddin kika sanar mata halin innar bello madu aizata tsorata kuma zata ji ta tsani surukarta daganan zaman lafiya babu kuma ni bello ne yafi banitausayi har cewa yayi ko zai fasa auren hanna ne saboda yasan tabbas zata hadu da halinmahaifiyarsa shi kuma a duniya abunda yaki jiniirin batawa hanna don yana sonta kamar yaddayake son rayuwarsa. Mun kada mun raya da innahauke ta hakura ta bar bello ya tare da amaryarsa agidansa taki fur wani uban ashar ta soka min ahe haushina take ji wai na dauki yata na bashi, ashetana so ta hadashi da wata shine yaki,Sum sum nayi na ficedaga gidan. Kuma wani abun bakin ciki shine belloyayi yayi ta yadda ya rushe bangarensa yayi nasiminti ya zagaye da katanga tace bai isa ba ana kasar zai saka amaryar tasa. Sai zana ya suyo yadanzagaye dakin su kwaya daya jal kuma abincinsu ahade dana yan gidan zasu dinga yi allah dai yakyauta mana nan mun dukufa da addu'a alah yadora shi akanta ta hakura ta barshi ya zauna agidansa hajir tace''amin nima zan taya hanna da addu'a amma caf wannan suruka ta hanna. Ai kogidan bazan taba takawa ba da sunan ziyara ni tunina yarinya tsoronta na ke ko gidan bana shigaallah ya sani banasan masifa. Duk hirar nan da sukeyi kakaf a kunnen hanna wacce ke daki tana jiyosu. Tayi ajiyar zuciya ta girgiza kai don tausayin kanta da kanta tace a ranta. Haka allah yaso danihaka zan kare a kunci, wahala da bakin ciki narabu da wahalar iya abu na fada wahalat innahaule allah kana sane dani, kasan halin da nakeciki kaine majibincin lamarina la'ila ha illa antasubhanaka inni kuntu minaz zalimin. Babana yayi gaskiya da yace babu mijin da zan aura da zairikeni amana in ba haisam ba. Baba baka sanyadda mukayi da haisam ba ka mutu ka barni akaninje in cewa haisam yazo ya aureni ka bashini, yayahaisam ya auri wacce yake so yar barni, baba kabarni a duniya baka san na rabu da haisam din bama. Ta rushe da kuka mai tsanani. Ta koma takwanta a tsakar dakin tana tunanin rayuwar dasuka yi da haisam shine farin cikinta a makarantabaya so ko kuda ta cijeta tattalinta wasa da dariyakullum har ya zuwa ranar rabuwarsu. Hanna tayikuka har ta gaji sannan ta mike don zuwa bandaki tayi alwala magariba. Ashe ta dade dayi bata saniba. Kamar yadda bello madu yace za'a kawo kefeda sauran kudade na al'ada an kawowa hanna lefeakwati uku kowacce a cike danma inna haule dukta rarrage kayan amma duk da haka masha allahan zuba mata kaya. A nan kauyen sai zancen kayan ake yi 'yan uwan hanna sai murna ake ammabanda ahmed domin ya tsorata da ganin yawanlefen nan yasan dole za'a zuba ido aga me kymaza'a kai dakin hanna.A matsayinsa na dan karamin malaminmakaranta firamare mai daukar dan karaninalbashi shi zai yiwa hanna gado, gara da kumaabincin 'yan biki gashi kuma a kurarren lokaci akasaka ranar bikin. Gashi duk danginsu shine maidama dama duk a jikinsa damgi suke nema. Yasan ko za'a taimaka masa da gudummawa bai wuce ayimasa fantekar alkaki da nakiya ba sai 'yankwanikan cin abinci wadanda suka daddage nezasu bashi setin samira. Da cin bashi da komaiahmed ya hada kudin gado mabi lamba one damadubinsa. Dan kudin da hajir take tarawa na dinkin hular da take ta bashi ya hada da sauran yargudummawar da ya samu ya sayi ledar daki dalabule shikenan sai kwanukan rabon abinci dasamira seti hudu aka haka aka jerawa hanna adaki. Bayan an sha biki an kai amarya dakinta tsaftsaf daidai karfinsu sai dai wani babban tashin hankali ahmed ta buga sama da kasa ya rasa kudinsiyama hanna gara. Don haka yace hajir da wasumatan suje su bawa inna haule hakuri insha allahukafin ta haihu za'a kawo mata gara don har ta farahabaici an kawo amarya babu gara. Kwanan hannauku cur tana rusar kuka bayan an kaita gidan miji . A ranar na hudun ne bello madu ya shigo dakintada jakar kayansa shi ma ya kauro gidan daga cangidansa. Da misalin karfe goma na dare gari yayishiru kowa yayi bacci abinka da rayuwar kauyeamma a zaune a gefen gado ya tarar da hanna tayitagumi tana tunani ido yayi mata jawur a kumbure , yayi mata sallama ta shigo. Ta daga kai da sauri tadube shi sannan ta amsa masa sallamar da yayimata. Ya shigo ya ajiye jakarsa a gefen akwatinantayazo kusa da ita ya zauna yana mai yi matamurmushi da nuna farin cikinsa a fili, ya dubikwayar idanuwanta yaga jawur don tsananin kuka da tasha yi yace'' hanna kukan ne har ya zamarmiki da idanuwanki haka ? Don allah ki daina kuka,hanna ni mai kaunarki ne bazan cutar dake ba'' tasake rushewa da kuka yasa hannu ya jawotajikinsa sai yaga tayi sauri ta zabura ta mike tsaye,Wannan zabura ta Hanna ta bawa Bellomamaki kamar wanda ya dona mata wuta, ya miketsaye yasa hannu zai rukota. Hanna tayi sauri tajada baya tana kokarin ta fice waje. Bello ya ce'' a.ahar waje zaki fice to na kyaleki zo ki zauna bazansake taba ki ba'' sannan hanna ta dawo tazo ta zauna a kasa kan ledar dake shimfide a tsakardakin ta hada kai da gwiwa tana kuka tamkarranta zai fita. Wannan kuka na hanna ya tayarwada bello hankali ji yake tamkar tana soka masawuka a zuciyarsa idan tana zubar da hawayen nan.Ya nisa sannan yace Hanna kiyi hakuri dan allah ki daina kuka meke damunki ne ? Nifa yanxumijinkine ki daina guduna kuna ina da hakkinakanki muddin kina guduna kuma kina kuka kinatayar min da hankali.Nace kiyi shiru kinki ki daina.Ko kina so inyi fushi dake Allah yayi fushi dakeMala'ikun allah su dinga la'antarki har sai gari ya waye? Hanna ta dago da sauri ta kalleshi yace yayakike kallona? Gaskiya nake fada miki ai duk macenda take gudun mijinta Allah da mala'ikunsa zasudinga la'antarta har sai gari ya waye ko kin yaddaki halaka ? Hanna ta girgiza kai tace bana so nahalaka'' yace ''to in ba kyaso ki halaka zo nan kusa dani ki zauna muyi yira. Cikin sheshshekan kukaHanna tace"kawu na zalunci kaina, na kumazalunceka da ban fada ma gaskiyar abunda yakedamuna ba. Kawu na kasance ina cikin wani hali natsananin damuwa wanda har nake tunanin bazaniya auren kowa ba. To amma dole nasan za'a yi min aure shi yasa na hakura na amince na aureka atunanina zan iya daurewa in zauna amma yanzubayan da akayi auren ciwon da yake damuna yadawo min danye bana jin zan iya zaman aure har insami aljannar da kowacce mace take nema akarkashin tafin kafar mijinki ta hanyar biyayyar aure. Kawu kayi hakuri ka yafemin dan allah karufa min asiri. Ka sauwakemin mu zauna haka batare da kowa ya sani ba, saboda sai in halaka idanmuka zauna a haka da igiyar auren ka. Bello yabude baki yana kallon Hanna can ya taso yazogabanta ya durkusa ya rike hannunta cikin yar siririyar murya mai dauke da tsananin dimaucewayace'' Hanna., fadamin ni kawunkine mai shirintaimakonki ta kowacce hanya kada kiji tsoronfadamin ko mene ne '' ta janye hannunta a hankalita share hawayenta tace '' idan bakamantaba a labarin dana baku a garinmu nace nayimakarantar sakandire da taimakon yaya Haisamson yaya haisam ne ya zame min dafi a zuciyatawanda dafin nan zai iya zamra min ajalina. Kawubello inason haisam harni ma kaina ina mamakin yadda kayi zuciyata ta kamu da sonshi haka nayiaddu'ar don allah ya goge mun , nayi azumi nayikukan kullum akan allah ya yaye min amma kamarkaramin ake . Daga karshe sai nake addu'ar allahya dauki raina da in dauwama a haka amma kaganni har yanxu a haka na rasa yadda zanyi'' ta rushe da kuka. Bello yayi shiru yana kallonta shimacan ya nisa ya ce'l hanna me yasa nazakiyi addu'arallah ya hadki da haisam ba kuyi aure kike addu'arallah ya yaye miki sonsa ko kua allah ya daukiranki? Hanna ta goge hawaye tace:: haisam yayiaure a ranar da mahaifina ya rasu'' bello madu ya gyara ya zauna a gaban hanna ya lankwashe kafadon jin labarin wannan rikirkitaccen al.amarin nahanna. Hanna bata boye maiba ta bashi labarintadana haisam tun daga ranar da babanta ya kaitamakaranta har ranar gidansu ta iske shi zai tafidaurin aurensa, daga karshe tace'' ashe yaya haisam ba sona yake ba taimako kawai yayi min nikuma zuciyata ta kamu da tsantsar kaunarsa donhaka ne a koda yaushe nake addu,ar allah yayayemun sonsa bana addu.ar haisam yazo yaaureni. Bello madu yayi murmushi karfin hali yace''haisam yana sonki yana kaunarki sosai fiye dani kaina da duk wni mai sonki a duniya. Akwai watamatsalar da tasa bai aurekiba hanna'' hanna cikeda mamaki ta kurawa bello ido tace me yasa kacehaka me ka gani daka fadi haka?'' bello yace''saboda ke yarinya ce shi yasa baza ki fahimcihakan ba, kuma nasan irin yadda kike hanna bawai haka ta taba faruwa akaina ba a.a inakwatanta nima rayuwata zata iya shiga irin wannanhalin da kika shiga idan na rasaki saboda kecewacce na taba jin ina so a duniya. Ni na yadda naamince zanci gaba da zama dake a haka amatsayinki na matata amma babu zancen saki a tsakanina dake saidai mutuwa ta rabamu sabodasanda nake miki, hanna da ace haisam yana jirankibayyi aure ba da zan daukeki ina kaiki wajenshiinaura miki shi don kiyi rayuwa cikin farin ciki, ni indawo gida in zauna ciwon son da nake miki yakasheni na yadda indai na ceto rayuwarki. Amma yanzu da yake haisam yayi aure kiyi hakuri. A cikinkashi dari bisa dari da kike yiwa haisam, ki daure kibani kashi daya a cikin dari har karshenrayuwarmu ta aure na gode. Hanna ki daure kicigaba da zama dani a haka kada ki barni ni dakeduka muyi biyu babu, kin rasa haisam ni kuma in rasaki'' yasa hannu ya jawo jikinsa zai rungumetatayi sauri ta mike tsaye ta juya masa baya. Ya tashi asanyaye yaje ya rufe kofa ya datse da makulli. Yayinda hanna taji wannan rana tamkar ranar damahaifinta ya rasu ta kuma rasa haisam yau gata adaki zata kwanta gado daya da wani a matsayin mijinta ba haisam ba, hawaye yaci gaba da tsiyayomata daga idanuwanta. Bello yaxo ya rungumetata bayanta yana mai sunbatar kunnuwanta dagefen kumatunta cikin sanyayyiyar murya hannatace'' a matsayinka na mijina akan babu yaddazanyi ka sami GANGAR JIKINA amma ruhi, zuciyata na wajen haisam.'' bai iya bata wannan amsan bacimak ya dauketa ya dorata a tsakiyar gado. Hannata shide tama fita hayyacinta saboda tsananin bakinciki yau gani ga wani daban zai fara saninta 'yamace kafin haisam wannan bakin cikin ne yayimata yawa yasa ta fita hayyacinta ma iya cewa suma tayi amma gogan naka baima lura ba ji yakeyau tamkar an masa albishir da gidan aljanna gashiya auri hanna harma ta mallaka masa GANGAR JIKINTA.A ranar da hanna ta cika sati guda ta fara saninhalin uwar mijinta ashe da kara take yi mata. Dasassafe ko tashi daga bacci basu yiba Inna Hauletayi dirar mikiya a bakin kofan dakinsu tana bugunkofar da karfi tana fadin a tashi haka baccin ya isaduk inda sati yayi an gama cin amarci bakunta ta kare kin zama 'yar gida fito ki dora dumame. Indozataje rafi debo ruwa.Firgigit Hanna ta mike ta dirodaga kan gado ta bude kofa ta fito. Ta durkusa harkasa ta gaishe da Inna Haule. A yatsune ta amsatace'' a tafi wajen murhu a dora dumame ga dawada gero can idan kuka karya kumallo keda indo ku surfa''. Bello yaji tamkar yayi ihu saboda takaiciyasan Hanna kuma ta shiga uku ta lalace kamanyadda amaryar Babansa Indo take dandana wahalakullum kamar baiwa.Ya tashi zaune ya rike kaitausayin Hanna zuciyarsa da tunani ina zai samomafita kafin ta zama baiwa, to amma babu wata mafita tunda har yau har waye war gobe innaHaule taki amince masa ya koma gidansa shidamatarsa. Da ya isheta ma da maganar sai tace dukranar daya sake rokonta akan wannan bukata tasaAllah ya isa kuma zata tsine masa, don haka Belloyaja bakinsa yayi gum. Haka hanna ta kasance tana yin iya kokarinta na ganin ta farantama uwarmijinta tana binta sau da kafa amma a banza innahaule bata gani. A koda yaushe zagin hanna taketana cewa.A yaushe zagin hanna take tana cewa aurendaba gara ma ai bai cika aure ba. Wai hanna tamallake mata da don da sai yayi sati biyu,uku baizogarin ba daga wajen aikimsa amma yanxu bayasati guda, zantuttuka barkatai marasa ma'ana daina nuna tsana tsagoranta. To wannan al.amari yasa hanna ta sake fitar da rai daga samun zaman lafiyaa rayuwarta, inna haule halinta daya da iya abukoma tafi iya abu ko uwarka ka yanka musu kadafa ka basu bazsu gode maka ba. Sai dai kawaiidan abun ya isheta ta shiga daki tayi kuka ta gaji.Idan bello madu ya dawo ya ganta a wannan hali sai ya shiga lallashinta yana bata hakurin nan nasababu abinda yake karama hanna banda takaici.Abu daya ya gano lagonta in har yana so tayidariya a duk halin bacin ran da take shine yacemata haisam. Haka yake sakata a gaba yace dolesai ta bashi labarin haisam. A koda yaushe hanna na kirga kwanikin yaushe bello zai dawo dagawaje aiki saboda dashine kawai take hira mai dadihar tayi dariya hirar ita ce hirar haisam.. Hanna daindo ne suke surfe a yau, inna haule ta fita unguwashine ma suka samu suna yar hira. Duk da indo tagirmewa hanna amma duk da haka bata fi shekaru ashirin da shida ba a matsayin suruka take a wajenhanna tunda matar baban mijinta ce. Amma doletasa suka zama kawaye. Hanna na bakace dusar,indo tana tikar dawa a turmi. Indo ta tsagaita dadakan tace'' hanna sai dai hakuri ni harna saba dawannan bauta haka Allah ya rubuto mana rayuwarmu. Hanna tayi ajiyar zuciya tace '' Allahyana barin bawanshi a halin daya so ya ganshi.Amma duk abubuwan da inna kemun bayadamuna irin duk abunda muke yi mata bata ganidubi fa irin aikin da mukeyi kamar zamu mutuyanzu idan tazo cewa zatayi munyi ha'inci bata surfu ba. Ga zagin da take yimin akan gara ni narasa yadda zanyi da rayuwata. Indo ta ajiye tabaryatace'' ai waike kina nufin duk abinda ake baki saniba a gidan nan yau? Hanna ta ajiye faifan dakehannunta ta tattara hankalinta gaba daya a wajenindo tana jiran taji me yake faruwa. Indo tace '' ko da yake kin tafi debo ruwa dazu da sassafe ni innahaule tasa na shifa dakinki na miko mataakwatinan aurenki guda biyu wadanda baki dinkakayan ciki ba tasa almajiri ya daukar mata wai zatakai wani gida ajiya tunda ba.ayi mii gara ba sumabaza ki daura lefansu ba. Daman wata uku ta daukar miki a kawo gara gashi yanzu kin shigawata hudu da aure . Don haka da zarar bello yadawo zata sa ya sakeki, lefen kuma ta kaiwa watayarinyar a daura masa aure da wacce zata kawomata gara. Kuma kinsan bello babu yadda zaiyiidan ta sashi a gaba tace '' ya sake ki . Hawaye ne sur yake zuba daga idanuwanta hanna ta mike dagudu ta shiga daki ta tara wayan an kwasheakwatina sai kwaya daya 'yar karamar kaya kalauku ne ta dinka a lefen su suka rage sai saurantsofaffain kayanta nada gasunan a kasa an watsarmata. Sai ta kwanta a kan gado ta fara rusar kuka hanna ta kware wajen iya kuka dan ko gasar masuiya kuka akaje ta duniya ina ganin ita zata zo tadaya. Can ba dadewwa inna haule ta dawo ta tarada indo ce kadai take aikin abincin rana tace'' inahanna? Indo tace'' ciwan ciki take tana daki. Taleka ta tarar da hanna sharkaf cikin kuka sai tace.'' babu wani ciwan ciki ba ciwan cikiba ko ciwannakuda kike kin bar gidan nan bazan iya ba harkartalauci anyi biki ko gara babu lefan dana dauke neshine yasa bakin ciki ya kwantar dake. Haka hannata yini cur a kwance babu ci babu sha sai kukaAllah cikin ikonsa sai ya jeho mata Bello da yamma kwanansa biyu ral da tafiya ba zato ba tsammanihanna taji sallamansa ya shigo, furgigit tayi ta tashizaune kallo daya yayi mata yasan akwai abindaaka yi mata har tasha kuka. Yaje da sauri ya zaunaa kusa da ita ya jawota jikinsa ya tambayeta mekedamunta take kuka. Ta amsa masa da ba komai . Ya ce yasan dole da wani abu kar ta boye masa ta fadamasa gaskiya, sai tace cikin tane ke ciwo, yayi shirushi dai ya jita ne kawai amma bai gamsu ba. Sai canaka jima hankalinsa yakai wajen akwatina yagabasa nan yace hanna ina akwatinanki suke? Tayishiru can tace inna ta kwashe takai ajiya wai tunda ba'yimin gara ba wata zata kaiwa ta aura maka itani ka sakeni. Sai ta rushe da kuka. Bello ya cije bakidon tsananin bakin ciki yayi shiru ya kasa maganasai yasa hannu yana goge mata hawaye ya nisayace. Daina kuka kece baki sani ba na baw ahmedkudin da zai saya mika gata kakaf yanzu ma cikon kudin da zai karasa sayyar na kawo masa. Damanyanzu zan koma wajen aiki tunda ina da aikin dare.Daman inna bata ganni ba ance tana makwabtabari inyi sauri in tafi baza ta san nazo garin bamaballe tayi min maganar sai ince Ahmed suyi kokarisu kawo garar gobe kinga an kashe bakinta kafin in dawo. Ya rungumeta hanna ya sambacikumatunta yace '' bazan sake kiba hanna ina sonkida yawa ki kwantar da hankalinki kinji ko, sannanya fice yana sauri ya tafi. Hanna ta bishi da kalloyayin da zuciya kece mata'' ba haisam kadai ba bello madu ma maisonki ne hanna ki kaunace shi.'' haka kuwa akayiwashe gari da misalin karfe uku na yamma saihanna taji an doso cikin gidan kamar a mafarkitaga kartan maza suna ta ajiye buhunhuna a kofar dakin inna haule . Mata suna ta shigowa dafantekun alkaki, nakiya dibulan da sauransu.Wannan al.amari ya bawa inna haule mamaki,nauyi da kunya saboda sunyi mata ba zata duk tabigari tana fadin ba.ayiwa hanna gara ba kuma bazasu iya yiba kwatsam sai ga gara wacce ko 'yayan attajiran garin ba'a taba yi musu gara mai yawanbuhunhunan haka ba. Nan dai inna haule ta haufara.ar borin kunya tana cewa ashe kuna tafe ku kaki sanar min nima in gayyato yan uwana suxo sutayani karbar irin wannan abin alhairi sannunku dazuwa ku shigo daki mana ya zaku zauna a waje. Hanna dibo tabarminki dana indo a shinfida baki.Ai da kun sanarmin zaku zo da nasa anyi mukugirke girke da soye soye irin wannan abin arzikihaka'' yan uwan hanna suka ce'' babu komai ai bazama muka zo yi ba mun kawo gara gata nan,zamu koma don yarmu ta sami salama a zamanta na aure da mijinta'' suma suka yaba mata ba dadi.Washe gari inna haule da sassafe taje ta debowahanna akwatinanta ta kawo mata amma ankwashe wasu kayan da yawa babu ta kumagargadi hanna kada ta sake ta fadawa danginta komijinta tayi shiru da bakinta. Da bello madu ya dawo faran faran inna haule ta kira shi ta nunamasa gara har tana cewa'' allah sarki ashe bakaramin shiri suke yiba shi yasa basu kawo dawuri ba irin wannan yawan gara sai kace yarsarkin noma ka auro '' bello yayi dariya ya ce'' Allahya sanya alheri ya bamu zaman lafiya'' ya nufi dakin hanna, bayan tayi masa sannu da zuwa ta kawomasa abinci da ruwa yasha sai ya jawo akwatinanya bude kamar yadda ya zarga tabbas mahaifiyarsazata kwashe wasu kayan haka kuwa ya gani takwashe kaya da yawa. Ya waiga ya kalli hanna saita sunkuyar da kanta kasa bata ce masa komai ba... Zaharaddeen Shomar Whatsapp 08168575100 GANGARJIKINSA NA AURA 2 Part 2 Posted by ANaM Dorayi on 03:14 PM, 30-Apr-15 Under: Gangarjikinsa ta Aura Yace '' hanna an kwashe miki lefenki ko? Kiyihakuri zan suyo miki wasu insha Allah idan muka yialbashi wani watan'' hanna ta dago cikin ladabi datattausar murya tace'' ni na yafe duniya da lahira basai ka biyani ba wahalar zata yi maka yawa. Kawubello babu abinda zance maka sai godiya da wannan gara daka yimin Allah ya saka da alheridomin ka kwatar min yancina tun daga ranar daaka kawo inna bata sake yimin gori ba. Yanzu zanyizaman farin ciki a gidan aurena: yayai murmushiyace'' farin cikin ki shine nawa Hanna, Allah ya karasanya ki a farin ciki fiye dana yanzu'' tace amin na gode. Karshen wata nayi da bello ya dau albashi saida ya sisiyawa hanna kayayyakinta damahaifiyarsa ta kwashe cikin dare ya kawowahanna a boye yace ai hakkintane dole ya biya ta.Hanna tayi godiya ta karba haka hanna da bellosuka kasance yana kyautata mata a boye komai ya gani na sakawa kona marmari sai ya suyo mata dadaddare ya shigo mata dashi ya bata a boye ba taredaya bari mahaifiyarsa ta gani ba. Bello yana karason hanna saboda ladabinta hankali da nutsuwada uwa uba tsananin hakurinta da tawakkali itakuwa hanna har yau har wayewar gobe ta kasa masanya gurbin haisam ta mayar da bello zuciyarta.Idan bacci take yi tana kwance da bello ammamafarkin haisam take. Idan tunani take yi haisamkawai take hangowa a zuciyarta. Tana kokarin tamayar da soyayyar da take yiwa haisam kan bellosaboda ita ma ta saka masa da soyayyar, sabida irin kyautata mata da yake amma abu ya faskara hakadai take dagewa tana nunawa bello tana sonsawanda a zuciyarta ba haka bane. Wasu lokuta dayawa idan suka tashi da safe. Bello yakan ce matayaya haisam? Don jiya kina kiransa a mafarki.Hakika hanna duk sanda ta kwanta mafarkin haisam take yi ashe har ambatonsa take a fili.Saboda tsananin son da bello yake yi mata ya yardaya amince kuma zai zauna da ita a haka. Bai tabanuna mata bacin ransa ba. Ita kuma hanna sai tajitausayinsa ya kama ta nauyi da kunyarsa talullubeta. Amma yaya zata yi tunda GANGAR JIKINTA YA AURA ZUCIYARTA na wajen haisam.Matsalar gara ta wuce tsakaninta da surukarta saikuma matsalar da inna haule ta dakko ta dorawahanna ita ce har yanzu hanna ko batan wata batayiba balle ta samu ciki fada da gori a wajen innahaule babu dare babu rana. Bello yayi kokari ya wayar mata dakai akan cewa ba laifin hanna baneciki Allah ke badawa amma abu yaci tura inna hauletaki ta saurarawa hanna cewa take ga sa'anninaurenta nan dukka ciki garesu wata bakwaibakwai tunda yanzu watan hanna bakwai da aure.Yau hanna tun karfe biyun dare take kai kawo a tsakar gida bacci ya gagari idanuwanta. Duk budeidon da bello zayyi sai yaga hanna tana fita ko tanashigowa cikin dakin kaman a mafarki yake ganinta. Can yaji ana kiraye kirayen sallar asuba tayi. Yasahannu ta laluba gefensa yaji hann bata nan. Yayifirgigit ya tashi ya fito tsakar gida ya hango hanna a gaban murhu tana hura wuta ya karasa inda takeyace.' Hanna yau lafiyarkikalau kuwa tun dare kike shige da fice kinki kikwanta yanxu da asubar nan wutar me kikehurawa? Hanna ta danyi murmushi tace'' kawu kamanta yau da duku duku oganka yace zai aiko damota za kuje Agadas shine nake dora maka ruwan wanka naji yau garin da sanyi sanyi''Yayi murmushiya ce'' Ai jinsa nayi kawai meye abun turo mota daduku duku sai kace zamubar kasar'' Hanna tace''Agadas ai da nisa shi yasa kuma wata kila bakwana zakuyiba ko ? Yace' Gaskiya agadas da nisaba kuma cikin garin zamu shiga ba local government zamu je ina ganin wajen 450 Km nekuma bana jin zamu kwana ziyarar aiki zai kaimucan mu kuma yan rakiya'' Hanna tace '' Allah ya kaiku lafiya ya dawo daku lafiya. Ina jin kiran assalatukafin ruwan yayi zafi ga buta ka fara yin yin Sallah ?Ta mika masa buta ta durkusa har kasa. Bello ya tsaya yana kallonta kawai saboda wata tsantsarsoyayyarta ce take kara sarke masa zuciya.Musamman wannan kulawa da ladabi da Hannatake masa, ya karbi butar ya shiga bandaki, kafinya idar da sallar Hanna ta hada masa ruwa wanka .Ya tashi ya shiga wanka. Kafin ya fito ta debo wankakkaun kayansa data wanke ta goge masa tadora akan gado ta goge masa takalmin da zai sakamar yadda tasaba masa kullum. Bayan yakammala yana goge gogensa da yan shafe shafesai ya dauko kayan da Hanna ta fitar masa ya saka.Tazo tana balle masa maballin wuyan rigarsa. Yayi murmushi yace'' Hanna na gode da irin wannahidima da kulawa da kike nunamin wannan yasaina kara sonki dari bisa dari, idan akwai soyyya datafi dari bisa dari ina miki Hanna sai dai ni anyakuwa na sami kwaya dayan nan kacal da nake so asanmin a cikin darin da ake yiwa haisam ?Cikin kunya hanna tace'' Haba daya kacal ai kafiguda daya'' yace '' a.a zancen gaskiya muke, nawaaka karamin ? Tayi dariya tace'' kawu ka wucegoma ma zaka kai sha biyar'' su duka suka tuntsireda dariya. Yace '' to tunda a wata bakwai na samigoma sha biyar nan da shekara bakwai zan iya tadda haisam'' suka sake tuntsirewa da dariya.Muryar inna haule ce ta katse musu dariyar da sukeyi tana bakin kofar dakinsu tana cewa'' tun dazumagana nake muku baku jini ba kun shige dakikuna tuntsira dariya da duku dukun safiyar nan tomotar ofishinku ce tazo suna ta kwankwasa gida . Daman Hanna abinda kika sani kenan ki shiga dakida miji kina dariya aikin kenan ciki fal kashi, babugurbin kwanciyar Da sai gurbin tarin kashi'' Hannatayi kasake yayi sanyi fara.ar da take yi ta koma cikiranta ya baci damin da ana siyar da ciki da ta suyohaka kuma da a wani waje ake nemoshi da taje ta nemo duk wahala koda kuwa zata mutu ne. Ko tahuta da zagin da gorin da ake yi mata. Bello yayiajiyar zuciya yace'' inna gani nan zuwa shiryawanake'' ta wuce ta tafi tana tsaki tana cewa'' Kaje kadawo dai daga tafiyar kazo mu zauna muyimaganar saboda bazai yuba, in zuba muku ido haka kawai aure wata bakwai kenan babu ciki baalamarsa kaina da kafafuwana turawa yarinyaabinci nake sai dai taci tayi kashi kawai. Ai ba dantazo ta cika mana shadda muka aurota ba mumamuna so muga dan jariri a gidanmu. Tunda tashanye ka ta asurce ka baka ganin lefinta to ni bata asurceni ba dole ka karo aure idan ma baza kasake taba, kai dole ma ka sake ta ka auro maihaihuwa don daki daya garemu a gidan nan'' Harinna haule tayi nisa ta juyo ta dawo ta tsaya a kofardakinsu Hanna tace'' Hanna kiyi ki fito daga dakinnan yau duk ke zaki yi aikin gidan nan shara wanke wanke surfe da girki ki fara debo ruwatukunna idan kin cika randunan gidan kakaf sai kifara aikin gida da yamma kuma kije gona ki tsinkowake da gyada dan sun nuna. Yau wacce kukeaikin tare indo aikenta zanyi magarya wajenkawata. Tunda ba ciki garekiba ba goyo ba ai wannan aikin bazai gagarekiba, sai dai idan kinjikashi sai kiyi a gonar tunda cikinki sai kashi babuhaihuwa. Kinga kuwa kashin naki ya zamar mintaki a gonar kinga kin taimaka kema'' Bello maduya fisata baisan sanda yace'' Haba inna ki dainayiwa hanna gorin haihuwa ba laifinta bane rashin haihuwa Allah ne yake bayarwa inna dama haryanzu Hanna ce take debo ruwa a rafi ina almajiriindana dauko aiki nace zan dinga biyansa. Ita taji daaikin gidan su kuna almajiran suje gonar. Hannatasa hannu ta toshe masa baki tace '' yi shiru karkasa taji haushina, mahaifiyarka ce babu komai duk zanyi aikin. Inna Haule ta rike baki tace'' inyedannan ka fara fada in fada dani akan matarkalallai abun babba ne jeka ka dawo ka sameni donwallahi ina ganin zamanka ya kare da wannanyarinyar mai kama da tumatir ina ganin rabaka takesotayi da kowa a duniya har dani dana haifeka . Ba'a haiyacinka kake ba na sani bayinka bane. Tatafi tana surutanta dai barkatai. Hawaye yana zubashar daga idon Hanna. Bello yasa hannu ya gogemata zuciyarsa cike da tsananin tausayinta ammayafi jin tausayin kansa da kansa. Saboda zaifi hannashiga wani hali,idanmahaifiyarsa tasa ya saketa don shine yafi sontafiye da yadda take sinsa idan ya rabu da hanna yarabu da farin cikin rayuwarsa. Kalma daya ce yasanidan yafadawa Hanna duk irin bacin ran da takezata yi dariya idan ya ambaci sunan Haisam . Yayi dan murmushi ya kalleta yace'' Hanna dama ace ayanzu kina da ciki ki haifanmun da namiji in sakamasa suna haisam. Hanna ta dago ta dubeshiidanuwanta a cike da hawaye sunyi jawur donkuka amma saida murmushi ya subuce mata a taketaji zuciyarta ta fara dan hucewa daga tsananin tafasar da take yi saboda kunar maganganun dainna Haule ta fada mata. Hanna taji wani dan sanyi aranta wani abu ya dasu a zuciyarta da bello yace ''dama ace ana da ciki ta haifi da namiji ya saka masasuna Haisam taji dama ace hakan faru mana. Ammadata tuna yanxu ma haka al'ada take don haka zancen ciki ma babu shi sai ta sake rushewa dakuka. Bello ya jawota ya rungumeta akirjinsa yanashafa lallausan gashinta yace'' Hanna lallai yauranki ya baci sosai har in kira miki Haisam ammakici gaba da kuka kiyi hakuri ki yafewa innata mucigaba da yi mata addu'a Allah yasa ta gane gaskiya Allah ya cusa mata soyayyarki a ranta. Hannatayiajiyar zuciya tace amin'' amma ka tayani addu'aAllah ya bani ciki kafin karshen watan nan inaganin haka zai saka soyayyata a zuciyar inna. Belloyace amin ya Allah, zan dukufa da addu'a kema kiyiAllah ya amsa mana. Ya goge matahawayen idanuwanta ya sumbaci kumtunta yace'' Haisamsunan danmu fa. Hanna ta kyalkyale da dariya tarufe ido sai taji wani farin ciki ya lullubeta. Tatsugunna ta jawo takalminsa ta fara saka masa akafa tana sake goge masa da tsumma. Ta feshemasa jikinsa da turare tace'' Kawu bello Allah ya kiyaye hanya kuje lafiya ku dawo lafiya. Yace aminHanna Allah yasa nazo na sameki lafiya cikin farinciki'' yana tafiya yana waiwayan hanna, itama ta fitohar bakin kofar dakin ta tsaya tana daga masahannu har ya shiga dakin mahaifiyarsa sannanhanna ta koma daki. A zaune a gefen gado Bello ya iske mahaifiyarsa tana tunani tana gayda kai yadurkusa ya gaisheta ta amsa a fusace ta fara masfada tace'' to dannan abunda nake so dakai shinekarka yadda kayimin musu akan duk hukuncindana yanke akanka ina nemar maka aure a gidandagacin garinnan yar sarauta ka dace ka aura tubda ka makalewa Hanna baza ka iya sakinta bato ta zauna anan gidan tare dani ita kuma waccamidan anyi aure sai a kaita gidan ka. Bello ya dagakai ya kalleta zuciyarsa cike da bakin ciki.Gidan da yasha magiya ta yarda akai Hanna takiyau gata da bakinta tana cewa yayi aure yakaimatarsa can amma banda Hanna ba. To ashe hannadin ta tsana kawai . Ya nisa yace inna me zai hanamu tare mu duka da amarya da hanna duk inhadasu acan din'' Ta girgiza kaia tace '' nace maka karka yimin musu ko? Haka naga dama, tashi kajeka dawo din mu karasa maganar amma idan kamatsa akan sai ka mayar da hanna gidanka zaka saince ka sake ta don wallahi hanna baza ta tare awancan gidan va sai dai idan bani na haifeka ba. Kobayan raina ka kaita can Allah ya isa'' Bello ya rike kai don takaici can yace'' Naji inna na gode, danAllah ki yafemin duk abunda nayi miki, idan na batamiki rai a rayuwata gaba daya''Tayi dariya tace ''Babu abunda ka taba yimin wallahi ko musun madaka tarka kake mun bayin kanka bane ta shanyeka ne na yafe maka Allah yayi maka albarka Bello ya mike ya fita hawaye ne shar yake fita dagaidanuwansa . Yana fitowa hanna tana jika gero tayisharkaf da hawaye daga gani ta gama jin dukmaganganun da suke yi. Kallo daya yayi mata yajihawaye ya sake kece masa. Yazo ya wuce tagabanta yace'' Hanna kiyi hakuri, ki sake yin hakuri, Allah yana tare da mai hakuri'' ta bishi dakallo tana hawaye yana waiwayanta yana hawayehar ya fice . Tayi shiru tana sauraren karar motarsuhar suka yi nisa ta daina jin karar motar, ta rushe dakuka tana cewa a ranta'' A bakin ciki ashe zandauwama? Yanzu aure inna zata sa kawu Bello zaiyi ya tareda amaryarsa agidansa ni abarni anan, meyasa inna ta tsaneni ? Me nayi mata tatsaneni? Meyasa kowaya tsaneni a duniyarnan ? Ubangijinayana sane dani, Allah kasan halin da nake ciki,Allahka fitar dani, Allah kaine abin godiya. Bayanfitar Bello madu da kamar awa guda. A lokacin hanna tana surfa gero, inna haule tana tsakar gidatana cin dumamen tuwo, indo kuwa daga wanka tafito zata shirya ta tafi magarya inda inna Haule zataaiketa. Suka ji ,Mota tururus ta tsaya a kofar gidansu.Wani ma'aikacine mai sanye da kayan 'yan sanda,yayi sallama ya shigo ba tare daya gaishe suba. Yace '' Nan ne gidan su custom Bello madu ko @inna haule ta tsaya dacin tuwonta tace '' Nan neamma baya na waye yake nemansa? Yace inazuwa'' ya fice, gaban hanna ya hau faduwa . Daf-daf daman tun jiya ta kasa bacci saifaduwar gaba take. Jingine tabarya da take surfe ta tsaya. Kawai ji suka yi ana cewa' ku kamada karfiwajen kafadan zaku rike inna haule ta zabura ta mike da gudu ta lekoHanna ma ta biyota da sauri idanuwansu sukagane musu wannan gagarimin tashin hankalin,Gawar bello madu ce ake shigowa da ita. Allahyayi masa rasuwa a sanadiyar hatsarin motar dayaritsa dasu yanzu-yanzun nan suna hawa hanyarsuta tafiya Agadas wata babbar mota ce tazo gwaramusu suka kutsa ta tsakiyar motar cikin ikon Allahbello ne kawai ya rasu, sauran sun sami munanan raunika suna asibiti. Hanna ta fadi ta suma,yayin da inna haule take neman tube kayan jikntadon gigicewa sai da aka rirriketa. kafin kace kwabogida ya cika yayi makil da 'yan uwa da makwabtamaza da mata. Ani masa wanka, an suturtashi ankaishi an binne kamar yadda sharia musulunci ta tanada. bello ya tafi ya bar rikici gidansa kuma shitasa ta kare a duniya domin rikicin duniya da mairai akeyi duk wani rai saiya dandana mutuwa Allahyasa mu cika da imani, amin. hanna tayiwa belloaddu'ar har yawun bakinta ya kame, idan ta ya gajida addu'ar ta rushe da kuka tayi ta huta haka dai har akayi sadakar bakwai 'yan zaman makoki sukawatse aka bar 'yan gida. yayin da bacci yakegagarar idanuwansu, kamar yadda inna haule takekuka cikin dare haka hanna ma sai ta laluba kusada ita taji ita kadai babu bello sai ta tashi tayi kukahar ta godewa Allah. kaico hanneta rasa kowa a duniya. hanna bata shiga. watamatsala batabangaran ci ko sha ko aikin gida ba har ta fitadaga takabarta.sai bayan ta fita daga takaba an fara zancenrabon gado sannan inna haule ta daka tsalle ta diretace babu abunda za'a bawa hanna na gadondanta tunda hanna ba haihuwatayiba da bello saidai ta hada 'yan komatsanta ta bar musu gida.kawu Ahamed yaji haushi sosai ya kuma lashi takobin ko sama da kasa zata hadesai ya kwatarwa'yarsa hanna hakkinta a tumuli takaba shari'ar shida inna haule har kotin koli idn bata bari an rabagadon nan da hanna ba. yace kuma babu indahanna zataje a gidan zata zauna sbd bello yana dagado a gidan ubansa, inna haule kuma tace ita kuwa baza ta bayar da dukkiyar belloba sai dai suzuba. makudan kudi kuwa aka kawo daga wajenaikin su bello, gashi da filaye da wannan tafkekengidan nan daya sha suminti da bulo. inna haulekuwa tace duk natae banda hanna ko sisi baza tabata ba tunda ko kwai bata saka a gidan ba. tashin hankali ya tabbata a zuciyar hanna ta rasa yaddazata yi da rayuwarta da kawunta zai hakura ya bariinna haule ta rike dukiyar bello dukka ba sai anraba da ita ba. duniyar nawa take wanda yatara ma ya tafi yabarta kowa ma mutuwa zaiyi. dukwani hango jin dadin. rayuwarduniya yagoge a zuciyar hanna babu abunda take bege sai mutuwatazo ta dauketa ta tafi ta hutaitama. daga gidankawu ahamed dake aiko mata da abincin dare darana. tafi tafiya suma wata rana basa aiko mata donyau da gobe sai Allah. hanna ta fara fitar dazannuwan daurawarta da kwanukanta tana siyarwa snnn taci abinci. wata rana da yamma daindo sunje rafi sun debo ruw suna tafe suna hira saisuka ji hassan me yekuwa yana sanarwa yanacewa "yekuwa. jama'a ga wata sanarwa, mai girmadagacin garin nan yace a sanar muku matawadanda mazansu suka rasu suka barsu da suzo fadarsa yanzun nan. ma'aikata daga nigeria sunzomusu da tallafin taimako. gwamnatin jihar kano anigeria ta aiko da taimakon kudi za'a raba musu jaridomin su rike kansu da marayin 'ya'yansu. ammakada wata ta kuskurataje idan ba mijinta bane yamutu, sai wacce mijinta ya mutu idon ta zunguri hana tace hanna muje wajen taron nan ko Allah zaisa mu dace. hanna ta rike baki tace babu ruwanmuyanzu idan mukaje ai mun shiga 3 a wajen innnacewa zatayi munje. mun tona musu asiri aci muka jemu tambaye tako zata yadda. a hanya sukadingahaduwa damata wadanda mazansu suka rasu suna ta tafiya gidan dakaci don karbarwannan tallafi mai tsoka. kowacce tagasu hannasai tace au, baza ku taho fada ku karbiwannantallafi ba daga nig fa bakin suka zo, indotace gaskiya hanna in baza ki ba ni zanje sbd idanmukakuskuramukaje gida inna haule baza ta barmu ba.amma idan mun riga munje mun karbobabu yadda zata yi damu fada ne dai da zagi yazama jiki. hanna tace to mu shigagidan. adama muajiye ruwa muje din daman gudun fadan inna nake,to kobabu abundamu kai ma kullum zagin mu takemuje kawai, suka shiga gidan adama suka ajiye ruwan da yake kansu suka nufi fada wajen taron.mata ne makil akan layi suma su hana sukajekarshen suka tsaya. wata kyakkyawar mata ce azaune akan kujera da tebur a gabanta an dorawasu fles akan teburin. kallo daya zakayi wa matarkasan tana cikin daula fatar jikintamulmul sumul. dukda matar ba fara bace amma ba baka bacekalarta mai kyau kayan jikinta kuwa ko ba'a gayamaka ba leshin zai doshi dubu hamshin sarkargwal da dankunneta da zubbunan gwal reras ahannunta guda hudu sai sheki sukeyi.matar maifaraa'a gata bata kyamar talakwa sai gaggaisawa dasu take suna yin hannu. tace. kowacce tazogabanta ta rubuta sunanta don asan yawansukuma nawa ya cancanta a basu. kowacce ta hauzara ido sbd basu iya rubuta sunanta. matar taceyanxu duk cikinku babu wacce ta iya rubutu tazo ta taimka min mu rubuta sunayenku?Hanna tayi shiru kamr tace ta iya amma gudunsurutun 'yan garin nan kar ace ta cika nuna iyawasai tayi shiru. Indo ta zungureta ta hanna bakn iyarubutu baki rubuta mana Hanna tace a'a indo baburuwana a samu wani yazo yayi dan kar ace nazogarinku na zake. Matar ta sake cewa To tunda babu wacce ta iya rubutu ina ganin ba zaiyu mu aiwatarda aikin da zamu aiwatar ba a yau sai mun nemowacce ta iya rubutu sannan saboda da mata zallamukeso mu kafa kungiyar dole mace ce zata zo tarubutu mana sunayen indo da taga kiri-kiri zasurasa bata san snda tace A'a ranki ya dade ga hanna ta iya rubutu" sauran suka hau cewa hannataimaka mana ke kuwa ashe daman kin iya rubuturubutamana karmu rasa Matar tace wacece hanna?Ta fito tazo nan Hanna taje gaban teburin matar tatsaya tace gani ranki y dade. Matr ta kalli hanna smada kasa wata burgujejyar doguwar riga wacce aka dinkintada wani wagambari mai kauri irin nddinnan itama kanwar kkrta ce ta bata, gashintatufke a tsakiyar ki tai gammo dashi da zasu deboruwa sai wani yalallen gyale baki ta yana akanta datakalminta dan madina akafarta. Matar tayimurmushi tace yaya sunanki? Hanna tace sunana Hanna Abubakar imam" matar tace HannaAbubakar kin iyarubutu? Hanna tace na iya ranki yadade, matar tace ko da yake ku anan french kukeyiba turanci ba ko irin na 'yan nig? Hanna tace ni nafiiya turancin nig, french din kadan-kadan na iyamijina yana koy min mtar taace , ta jawo kujera kizo nan kusa dani ki dinga rubuta sunayen su, ki fararubuta sunan ki sannan ki rubuta sunayen sauran.Hanna ta zauna tana rubutu sunayen matan nandaya bayan daya suna tahowa a layi. Ta gamatubuta sunayen sai magaruba tayi sai aka tsayar dashawarar sai gobe da safe su kra taruwa dan a raba musu tallafin sukanufi gidanjen su, matarkuma gidan dakci aka kaita a can zata kwana,namijin kuma da sukazo shima aka kaishi wanigida aka suke shi tunda dare yayi dokin gobe tayisu koma fada. Hann da indo kuwa sai suka haufaduwar gab suna shirya kalmar da zasu furta wajen kare kansu daga fadan inna haule. Aikuwadaga shigarsu gida ta fara yi musu fada donlabari ya kai mata cewar anga su hanna a fadasunje karbar jari. Tana cewa dole Hanna ki barmingidana sbd so kike ki koywaindo kinji da fitinawanda da bata iyaba, ki tafi can gidan ku acan ake yunwa ake neman jari mu nan Allah ya rufa manaasiri,kema indo tunda wanda ya du nuyinki ke da'ya'yankiya rasu bello ne damn yace shi zai dingaciyar dku gashi ya mutu dole kema asan yaddaxa'ayi idan bangaren gidanku zaku siyarmin to,idan ma wani zaku siyarwa dai duk daya ki karbi kudinki ki kada 'ya'ynki ku koma can Tawa localgobernment grinku. Ba zaku zo ban haife ku bakusamun hawon jini tunda kun hallaka mazan nakuni dai ku kyale ni. Washe gari da sassafe su hnnasuka tashi suka hu aiyukan gidan,bayn sun gaamsuka leka ko ina basu ga inna haule ba ta shiga makwabtasai suka debi bokitansu suka cewamasa'ud dan gidan indo in inna tazo yace mata suntfi deboruwa . A tamfar. Maikyau hanna ta daurabasu tsaya a ko ina ba sai a fada wajen taro, sunmadanmakara don ynzu tar da rabi wjen taro, sunmadan mkra don ynxu tara da rbi tayi suka ajiye bokitansu a lungu sukaje wajen taron matr ta. KalliHanna tyi murmushi tace hanna ke muke jira kifarakiran sunaye in rarraba muku kudin . Hanna tagaisheta faram faram da fara'a sannan ta krbitakardar ta. Fara kirn suna tace Hanna abubakariman ce ta farko, matar tace to ki kira sunayen daya bayan daya suzo subi layi sai kwai in dingamimmika musu kudin a layi Hanna ta fara kirnsunayen, kowace tan zuwa tana shiga layi kamaaryadda sunayen suke a jikin takrdar,byn hanna takammala kiran sunayen sai matr t mike tace tomadalla Assalamu Alaikum jam'a su duka sukace wa'alaikussalm tce ni sunana Haj Hindatu umardaga kano state nigeria. Nazo nan grin mai sunaDashi karkashin karamar hukumar mgarya a.Janhuriyar niger don in kawowa 'yan uwana matatallafi da taimako yaddamatan da suke da mazasuke samun taimako daga wajen mazajensu to ku da baku damazasai kusamu san'ar da zakutaimakawa kanku da marayin 'ya'yanku. Sukasatafi raf'-raf suna cewa Allah ya saka da alheri mungode hajiya hindatu. Ta cigaba da cewa dagagwannatin jihar kno matar maigirma gwamanjihaar kano ta bude wta kungiya wacce za'a dinga taimakwa matan da mazansu suka rasu sukabarsu. Shine taga ya dace mu shigo makwabciyarkasarmu Niger suma mu hada kai da gwiwamutaimaka musu saboda Abunda yayi nigeria shiyayiniger duk uwa daya uba daya muke, tafi sukahauyi suna murna suna cewa Allah ya kiyaye Nigeriada gwannatin jihar kano Hajiya Hindatuumar taci gaba da cewa yanxu anan garin zamukirkiro wani suna mu saka wa wannankungiyatamu. Don mucigaba da turo muku tallafi tako ina daga kasarmu. Bani za bawa kungiyar nansuna bku d knku ykmt ku saka mata suna. Nan dai wannan tace a sa mata kaza wacce tace asa mt kazadaga karshe di. Suka tsayr da shawarra akan asawa kungyar sun hindatu umar, tayi darya tace a'aba sunana za'a sa ba sbd wata kila baz ku sakeganinaba saidai kuga an turo muku wata sbdmuma acan 'yan kungiyar muna da yawa idan aka turoni yaugobe wata za'a turo muku. Amma yanzutunda ga wacce taiya rubutu da karatu hanna itazata dinga wakiltarku idan ta kama mahar cannigeriazata dinga zuwa tana karbo muku tallafi inaganin idan kun amince asawa kungiyar sunnhanna. Gaba daya suka hau cewa mun amince asa sunan HANNA,Dagakarshe matar ta jawowata jaka ta fara mikamusu damin kudi kowcce kudin data samu idanaka kiyasta dakudin nigeria zaiyi kimanin nairadubu sha biyar-biyar. Bayan kowacceta karbataceba'a kare ba.akwai atamfofi da wasu kudadenda za'a sakebasu shima daga gwannatin nigeria saidai basu zo dakudin yanzu ba amma idan zaiyusu nada wata daga cikinsu da zataje ta wakilcesudan taga waje tacigaba da zuwa su sai suka hadabaki suna cewa mun wakilta hannaa matsayinwakilyarmu. Hjy hindatu ta juya ta kalli hanna tacekin amince hanna zaki bini nigeria kidinga karbo musu taimakon? Hanna tayi murmushi ta ce hjymezai hana sai in biki din akan haka sukayi sallamacewar hanna zata bi hjy hindatu kano don karbomusu wasu tallafin masu yawa,kafin hanna tabimatar saida taje da sauri gidan kawu ahmad tashaidamasa duk sha'awarda sukayanke akanta ya amince ya kumayi mata fatan Allah yasa su dauketaaiki ma acan tayi yace idan da sarari tajemakarantarsu takarbo sakamakon jarabawarta tanemi aiki ko Allah yasa ta dace. Ta rabakudintagida 2 ta bashi rabi. Ta sake rabanata gida 2tabawa matarsa hajir. Kogidan inna haule bataje ba dauko kayanta kawai ta fada motar su hjy hindatuumar sai tafiya daman hjy hindatu tayi. Sallamadagaci dasauran hakiman garin tabasu kudi masuyawa sumata sanar musu zata tafi da hanna dontasake karbo musu wasu kudaden taimako. Sunyimurnasosai sun shi albarka sunyi musu fatan Allah yakiyaye hanya. Mutumin da sukazo dashimai sunashehu shine yake tuka motr hjy hindatu a baya tazauna hanna ce ta zauna a gidan gaba, motar kirarhumma jeef dindimemiyar motamai dauke darundumemyar rikoda an saka sauti mai tashi a hnklsai sanyayyiyarna'urar sanyi ce ke dukan jikin hanna. Cikin motar ma abun kallo ne lallausankujerun motar su suka sa hanna ta nutsu komagana bata iyayi,tace a ranta Allah ya baku duniya wannanmota ce kawai ba gida ba, Allah mai azurta wandayaso sun hau titi dodar suna zuba gudu a titi saihanyar kan karfe 3 ma a ciki garin kano tayi musutafiya suke kamar bayi sukeyi ba sbd babu watakura ko gjy irin ta matafiya a tare dasu. Hanna sai kaallon kano takeyi galala komai yaci gaba bakamar lkcn da ta zo ba. Babu abinda ya fado mata arai sai ranar data zo wajen haisam zuwanta kanona farko kenan kuma bata taba ska ran sakedawowa ba ashe zata dawo yanzu Allah ya kawodalili. Ta dinga kallon haanyoyi ko zata gane gidan su haisam amma ina ba tama gane hanyar ba balleta gane gidan. Haism haism take kira a zuciyartayayin da kwalla ta cika mata idanuwanta. Tamadubi hjy hindatu take kallonta tace hanna yayadai naga kamar kwalla ta cika miki ido ko iskar ACce tyi miki yawa a ido a rage? Hanna tace a'a babu komai suka cigab da tfy can hjy hindatu tace hannaga garinmu fa, kano kenan kin taba zuw kano netunda naga kamar a nigeria kikayi karatu? Hannatace nan FGGC kazure nayi na taba zuwa kano saudaya sheraka 2 da suka wuce amma bazn iya tunaina ne unguwar dana zo ba, sulemanu cresent sunan unguwar , hjy hindatu tace oh sulemncresent sunan unguwar ai bamu da nis sosai ynxumun ahmdu bello way zamu bi ta wajejen dai ni asokoto rd farm center nake zan nuna miki kwanarhanna tace to suka cigaba da tafiya.Daidai get din wani tsantsereren katafaren gdamotar su hanna ta tsaya yayin da mai gadin ya tasoda sauri yazo ya bude musu. Hjy hindatu ta kallihnna tce hanna nan gidana ne ina so muyi sallamuci abinci mu huta wajen gobesai in kaiki wajenkungiyar subki tallafi a kaiki can garin naku ko? Hanna tace babu komi na gode hanna taga duniyawannan gida shine ake kira aljannar duniya sbdkana shiga farfagiyar gidn wasu fulawoyi ne anzagaye wani dan tudu yana ta bulbulo da tsuntsayemsu kyau aka watsa a farfagiyar gidan sunt t yawocan gefe kuma wajen wnke ne (swimmingpool) an kewye da wasu kujerun hutawa cn gefe kumawjen wsannin ne ma motsajiki (games) wajenbsket ball, tble tannis, football da sauransu. Iskuma gawta tafkekiyar kofa wacce zata kaika cikingidan. Daga can bay kuma boyi quarters ce itamakamar wani katfaran gidan. Arziki ma anan ai ba'a magn kai kce a turai kake ba'a nigeria ba. Hjyhindatu ta yukura zata fita dagcikin mota ta juya takalli hanna wacce ke zune tayi turus tace hnna fitoman hanna tj kofar zata bude ta kasa sai da hjyhindatu ta fito daga kujerar baya tabude mata tawaje snn hanna ta fito, gidan ya baw hnna sha'awakwrai da gaske. Tace hjiya gidanki yayi minkyau wlh, ta kalli hnn tayi murmushi tace nagodehanna.Wani dogon saurayi ne kyakkyawa a gefe azaune akan wata kujerar roba yayi tahumu ya rikekai. Hjy hindatu taje ta sameshi tana zulayarsa tacemijin me akayi maka yau? Kana ganina ko ka dagokayimin magana ko budurwarce ta baka maka rai?Daga nan hanna ta tantance kanin mijinta ne wasan kanin miji take yi masa, ya dago a sanyaye ba fara'ada kyar ya kalleta yace antynah muje daga cikimuyi mgn. Hjy hindatu t kyal kylle da dariya tace kaidalla rago nasan fada ku kayi kai da ummi dukydda kayi. Yace wannan me sauki ne muje ciki dai,ya juya ya halli hanna yace anty wacece wannan? Tace yar niger ce yace niger? Daman niger kike jeyau kwana 7 bakya nan ? Tace eh ehmuje ciki dai,hanna zo mu shigo ciki. Suka isa wani tafkeken falowanda zan iya kiransa aljinnar dunita anan hjyhindatu ta ajiye jakarta akan kujera ta kshingidadon gjy. Tace da hanna zo ki zauna bakuwa kema kin gaji hanna tayi murmushi dukka snsan jikintaya dau sanyin na'auraa, a fakaice kallon alatun dasuke jifge a falon take take tana tambayar zuciyartaabunda bata sani ba bata taba gani ba. Saurayinyaje wjen wata (telephone) waya da take sakale ajikin bango ya dauka yana latsa wasu lambobi can da aka jima yace" hello hjy ga aunty ta dawo ashewai niger taje. Hjy hindatu ta tshi zune tace lhhajiyrku kake gayawaa ashe niger naje damanhaka kake kai in an gaya maka magana sai kafada? Yazo a sanyaye ya zauna akan kujera yaceaunty dole fa hjy tsn kin dawo kuma in kika je tunda neman ki ake yi tuntuni "hajiya hindatu tacehjyr a asibiti take ko kuma a ofis? Yaya mai jikin inata tambayarka baka bani amsa ba? Yace yana canyaji sauki tace bari. Inje inyi sallah inje in duboshi,hour yanzu basu sallameshi? Yana premier hospitalko Aminu kani aaka mayr dashi? Ya ce yana can dai. Tace wai meke damunka ne duk da kyaar kkemagana na lura. Hanna tace wani ne bashi da lfy?Allah ya sawake. Hjy hindatu tace wlh mai gidanane bashi da lfy yana asibiti. Hanna ta girgiza kai tacekai kai Allah ya sawake masa, ciwon ya tsananta nehaka har da kwanciya a asibiti me ya same shi? Tace ciwon a zuciyarsa yake ciwo ne sosai yakefama wallahi hanna. Hanna tace zuciya? Is tarableAllah ya bashi lfy. Ramlah tace amin shigo gabandaki muyi sallah ko azahar bamuyi ba gashi 3da rabi yanzu la'asar ta kusa. Hanna na biye da itahar wani katafaran daki mai dauke da wani kayataccen gado a ciki dakin kuma da wanikyataccen bandaki. Hjy hindtu tace hnna ta shigabandaki tayi alwalla idan ta fito sai ta shiga . Hannata shiga bandaki sai da tasha kallo ta gaji sannantayi alwalla ta fito. Hjy hindatu mata shiga ta dauroalwalla.Suna idar da sallar azahar sai kwai suka yi l'asardon lokaci yayi hnna na tahiyar karshe hjy hindatuta idar tana jan carbi suka juyo na rafsa kukakamar na mutuwa a babban flo a guje hjy hindatuta fita hanna kuma ta hau sauri tana so ta idar tajeitama taga meke faruwa hanna taji ihun ya kara karuwa da hjy hndatu ta fita kuka wiwi sukeyi.Hanna ta fita da sauri ta iske mata makil a falo anata kuka. Hanna tayi kasake tana kallonsu bata sanme ya faru b balle tasan me zata ce musu. Hjyhindatu ce ta taso tazo ta kama hannun hamma takawo ta tsakiyar matan nan wadanda suka doshi su ashirin. Hanna ta durkusa akan kafet ta gaishesuwata kamillliyr datijuwa mai kyau ta dago da luhu- luhun idanuwanta ta dubi hanna ta juya ta kalli hjyhindtu tace ramlah wacece wannan? Tce wannanitace hannar haism. Su duka suka bude ido da bakisuka ce hanna, hanna ce wannan ina kike nemota? Ta rushe da kuka tace har niger naje na nemota saigba daya ka rushe da kuka. Hanna ta kasa ganeabunda ake nufi, knta ya daure abunya batamamaki. Tce meke faruwa, a ina nake anan? Hajhindatu ta goge hawaye tace hanna nan kano ne.Ta nuna wannan dattijuwar matar tace wannan itace mahaifiyr haisam! Hisam! Haisam haj hindatuta ce haism. Ta nuna wannan saurayin tce wannanizziddin kanin haisam ne, ni kuma ba sunana hjhindatu ba, sunana ramlah nice matar hasamhanna ta zabura ta mike tsaye tace ramlah, mekefaruwa, me nayi miki? Ramlh ta jawo hannun hanna ta zaunar da ita tace zuna hnna zan bki lbrnhism ynxun nan, hanna ta koma ta zauna asanyaye ta tattara hankalinta baki daya a sauraronramlah,Ramlah ta sharbehawayen da suka cika mata ido tace hanna, hisan,yana sonki, haisam ne mai sonki, babu wani maisonki a duniya irin hisam. Haisam yafi kowakaunarki a cikin duk masu sonki a duniya hannatace ramlah meyasa kika ce haka? Ramlah tace abunda yasa nace haka shine haisam bai taba yinsoyayya ba sai akanki, bai taba ganin wata 'yamace ba a duniya da yaji yana sonta kamarkihanna, hanna ta dago ta kalli ramlah tace ammahaisam ke ya faraa kafin ma mu hdu dashi houryayi miki alkawarin zai aureki. Ramlah ta girgiza kai tace hiasam ya sanni tuntuni amma ba sona yakeba. Allah ya jarabeni da tsananin son haisam tunmuna america idan sunje hutu gidnmu. Nashasanarwa mahaifiyata sai tace kada ma in fara bazaiyiwu ba, saboda mhaifiyar haisam kaawarta cetasha gaya mata cewa haisam bashi da ra'ayin soyayya yace shi bai taba jin yana son wata bakuma yana ganin bazai taba ji ba, har muka dawokasar nan. Amma naki hakuria naci gba da cusasoyayyar haisam a zucyata, na dinga kokarinnunawa haisam irin soyayyar da nakeyi masaamma sai yake nuna min baisan abunda nake nufi ba. Da nag haka sai na dinga bin ta hanyr iyayenmudon na sami haisam, da farko mahaifina na samunasa masa kuka cewar in ba'a bani haisam b xankashe kaina. Mahaifin ya lallashe ni ya ce duk maisauki ne zi sami mahaifin haisam. Haka kuwa akayimhaifina yaje ya sami abokinsa mahaifin haisam ya shaida masa bukatata. Sbd da sanin raa'ayinhaisam akan soyayya bai amsa masa ki tsaye basida yace zai tuntubi haisam zai kuma yi shawarada mahaifiyar haisam kusan shekara guda bamujiwata cikekkiyar msa ba daga gidansu haisam to sainasan haisam yaki amincewa ne yasa babu wata cikekkiyar amsa da naji game da bukatata akannifa har yanxu ina son haisam, babu irn kalmar damhaifina bai furta min b wajen wayar min da kaiakan in cire son haisam, in so msu sona ga sunnbarktai suna zuwa, naki nace lallai-lallai sai haisam,Nazo nyi yjin ikin cin binci naki ci naki sha naakaura daki sai kuka. Iyayena suna ta lallashina nkicanj ra'yina. Shi kuwa hisam bai san ma abindanakeyi ba, yn can jami'a yana karatunsa. Kawrkirauda kanwata nake aike da wasika in shaidwhaisam halin da nake ciki amma bai taba bani amsar wasikata ba. Ko dda naje gidansu bayacemin komai koda zamu yini tare ko uffan bazaicemin ba. Haka idan yazo gidanmu wajen auwalyayna abokinsaa idan muka gaisa babu binda zaisake cemin ko hira nake musu bai cika sa baki ba.D mahaifina yaga na dmu sosai da son haisam shine ya sake samun mahaifin haisam suka zaunasukayi magana sosai mahaaifina y nunaa bacinransa yace b yadda za'ayi suce haisam yakiamincewa tunda bashi ya hifesu ba, susukahaifeshi in har suna so zasu san yadda zasu sshi yaamince dole. Gudun kada abokantarsu ta baci mahaifin hisam y kira haisam yace ko yaki. Koh yaso is ya aureni, da farko mahaifiyarsa taki tacebayayiwa a yiwa namiji auren dole abarshi tundayce bashi da ra'ayin soyayya gashi yanzun kara2yake a lkcn yana shekararsa ta karshe a jami'a.Mahifiyar hisam tag dai abun zai koma tashin hnkl tsakanin ta da mahaifana da kuma mijinta sai taamince tace ayi auren, taci gaba da lallaba haisamakan ya yarda ya iya bikin. Da aka zo sa ranarauren yy habib sai aka had damu. Aka sa ranaraurenmu shera daya dai daii lkcn da haisam zaigama bautar kasa ni kuma na gama sakandire sai ayi bikin. Har lkcn da ka sa mana rana haisam baitaba zuwa gidanmu ba da sunan yazo zance. Nicekullum nake yi masa waya musamman da tsakrdare. Yan amsa mun wayar amma wani lkc sai yyibarcinsa m ya barni a layin wayar ina magana nikadi. Hak a cikin hirarrakin da muke akwai wasu tambayoyi da nake yi msa bi tba amsa mun ba sidiyyi shiru. Tambyoyin kuwa shine hisam ynxunkuw kana jin sona a zuciyarka? Meyas baka zuwgidanmu znce? Idan ban ganka b ko naji muryarkabana iya barci kaifa? Baya amsamin duk watatambay data jibanci soyayya, n sni kuma n gane haisam b sona yake ba kiri kiri amma idona ya rufetunda ni ina sonsa zan iya zama dashi a haka.Haisan yana bautar kasa. FGGC kazaure ina gidainaa jirns ya gama sai ranar daurin aure a bda dasadaki in zama matarsa kwi ya rage. Kwatsam sahaisam ya kammala bautar kasa sai yace shifa yakammala butar kasa sai yace shifa ba ynzu za'ayibikin ba ayi na yay habib tunda shine babba ayi namu daga bya. Aka yarda da bukatar haisamtunda lallabashi akeyi akayi bikin yaya habib. Iskwi mukaji haisam ya koma FGGC kazaure amatsayin cikakken malami wi shi koyarwa yakesoyayi shiyasa ya nemo ikin can, nace na yarda ayibikin zan iya binsa kazaure mu zauna, hk dai haisan yayi tayi mana hanya hanya yaki yarda yibikin. Da yaga an takur masa ance sai ya barokazaure ya dawo kano ga kamfanin babansa ananzaiyi aiki ayi bikin mu kuma shi yace shi ya aminceidn na sami wani na aura don shi kuma sai nan dashekara 5. Nace na yarda zan jira shi in shiga jami'a kafin nan nima na kare sai muyi auren kawai. Ranmahaifina ya baci mahaifiyatata zazzgeni tace bazanjira shi ba sai kace bani da zuciya wanne irin so newannan. A lokacin akwai wani saurayi nai sunaDalhatu dan jarida ne yana sona sosai. Yana so yaaureni nace ni bana sonsa bazan aureshi ba daidai lkcn nan an turashi BBC london yace idan anyibikinmu sai. Ya tafi dani can london nayi kara2jami'ata, naki fur. Babu irin nasihar da iyayena basuyimin ba da lallashi naki ji nifa idan ba haisan basaidai in fsa aure. Iyayen haisan. Ma sunyi iya.Kokarinsu wajen tlastawa. Haisam ya dawo yazo ayi. Bikinan namu sai ya daina zuwa wkend din mada yake zuwa kwata kwata. To. Kowa. Ya rasa.Yadda zaiyi damu suka zuba mana ido Sai addu'a.Haisan yana bautar kasa. FGGC kazaure ina gidainaa jirns ya gama sai ranar daurin aure a bda dasadaki in zama matarsa kwi ya rage. Kwatsam sahaisam ya kammala bautar kasa sai yace shifa yakammala butar kasa sai yace shifa ba ynzu za'ayibikin ba ayi na yay habib tunda shine babba ayi namu daga bya. Aka yarda da bukatar haisamtunda lallabashi akeyi akayi bikin yaya habib. Iskwi mukaji haisam ya koma FGGC kazaure amatsayin cikakken malami wi shi koyarwa yakesoyayi shiyasa ya nemo ikin can, nace na yarda ayibikin zan iya binsa kazaure mu zauna, hk dai haisan yayi tayi mana hanya hanya yaki yarda yibikin. Da yaga an takur masa ance sai ya barokazaure ya dawo kano ga kamfanin babansa ananzaiyi aiki ayi bikin mu kuma shi yace shi ya aminceidn na sami wani na aura don shi kuma sai nan dashekara 5. Nace na yarda zan jira shi in shiga jami'a kafin nan nima na kare sai muyi auren kawai. Ranmahaifina ya baci mahaifiyatata zazzgeni tace bazanjira shi ba sai kace bani da zuciya wanne irin so newannan. A lokacin akwai wani saurayi nai sunaDalhatu dan jarida ne yana sona sosai. Yana so yaaureni nace ni bana sonsa bazan aureshi ba daidai lkcn nan an turashi BBC london yace idan anyibikinmu sai. Ya tafi dani can london nayi kara2jami'ata, naki fur. Babu irin nasihar da iyayena basuyimin ba da lallashi naki ji nifa idan ba haisan basaidai in fsa aure. Iyayen haisan. Ma sunyi iya.Kokarinsu wajen tlastawa. Haisam ya dawo yazo ayi. Bikinan namu sai ya daina zuwa wkend din mada yake zuwa kwata kwata. To. Kowa. Ya rasa.Yadda zaiyi damu suka zuba mana ido Sai addu'a.Na shiga jami'a a nan kano BUK ina karantar.Bangaran lbrn 'yan jarida (mass com) ina Karatunaina jiran haisam na sami samari kalakala akwaikyawawan da suka fi. Haisan kyau nesa ba kusaba, akwai masuarzikin da suka fi haisam, masusona fiye da haisan amma. Na kisu ni sai haisam don bazan mant ba har mahifiyt tke cemun zakiauri haisam in n takura masa mma bazaki samisoyayyar da kike nema ba. Nce idan anyi auren zaisoni ai. Nasa kanwata rauda ta binciko. Mun wanneirin buri ne haisam ya kudira a FGGC kazaure yakeso y cika kamr ydda kullum ake cewa, rauda tace ai wata yarinyace year jinsu mai suna hanna yacekanwarsa ce tana jin sbd it yaki barin mkrntr nasrauda taci gaba da lura d binda yake gudanatsakanin hasam da hanna kuna ji 4 (ss1) rauda tzomun da cikekken bayani game da binciken danasata tayimun. Tace abu ya tabbata haisan son hanna yakeyi,duk mkrt an sani zance ya fito fili. Tabani lbrn irin gwagwarmayar da akayi tsakaninhaisam da malai masu takurawa hnna da dalbaimasu takura miki yaya habib ma ya fada manayadda sukayi da haisam har hisam ya wawaroadda kamar dabawa masa, yaya habib yace haisam sai addu'a sbd kamar ya zautu a son wata yrny donhaka nema yaki dawowa.Raina ya baci sosai da naji nce haisam yana sonwta, na lashi takobin ko wacece wannan hanna saina ga krshent ko a ina take, shine nabi direban muda zai dauko rauda ranar hutu don inga wacecewannan hanna? Kuma 'yar waye? Dame ta fini dahaisam yafi sonta dani? In kuma ja mata kunne akan ta rabu da mijina, don alkcn yadda nakeji zaniya hallaka duk wanda yake kokarin ya rabani dahaisam, naje mkrt na tarat bakya nan ance suhaisam sun tafi dake sai muka biki garinku mukatarar bakya nan sai mahaifinki. Na fadimagangannu iri iri a cikin bacin rai sbd mahaifinki ya rabaki da mkrtr don ki rabu da haisam, haisanbai bar kazaure ba is da kika gama mkrt da sati 2snn ya dwo gida da kaynsa, mahaifinsa na ganinsacewa yayi haisan har ka cika burin daka kudira kadawo? Haisam yayi murmushi yace eh baba,mahaifiyarsa tace idan baka gama cikawa ba ka koma ka gama ka dawo ramlah na jirnaka ayi bikinku, haisan yace ya gama saidai kuma yazo wajensuneman alfarma guda daya donAllah su taimakamasa , suk bukaci haism daya fadi abunda yake soya fada inshaa Allahu idan bta fi karfinsu ba zasuyimasa sai ya zauna ya basu lbrn ki tas tun daga ranar da aka kawo ki mkrt har halinda kike ciki agidanku, ya kuma bayyana musu tsananin son dayake miki yace su taimake shi su bashi izini yahadamu mu 2 ya aura sbd kece rywrsa zai iya shigawani hali idan suka ki amincewa masa, bai rufebakinsa ba mahaifinsa ya daka masa tsawa yace bazai yuba karma ya sake yi musu wata magiya.Mahaifiyarsa ma tace in har ita ta dauki cikins wata9 ta hifeshi yasha nononta har ya girma to bataamince masa ya auri hanna ba.Kwana 2 haisam ya kara ramewa kullum kagnshi yana tunani kallo 1 zakyi masa kasan yanacikin wani hali na tsananin damuwa, ya daina ci yadaina sha balle yayi hira da mutane mahaifinsa dayaga haka sai ya kira shi yce yaje ya sameni yayimin bayani akan ko zan yadda ya auremu mu 2 idan na mince to zaije ya sami. Matarsa mahaifiyahaisam ya lallashet ta yarje masa, haisam ya samenia lambun gidan mu da yamma. Yake cewa intaimakeshi in ceto rayuwarsa ya auremu mu 2 ni dake, na kekashe kasa nace ban yarda ba, hism yadurkusa gwiwoynsa 2 a kasa yana rokona ina duba girman Allah da tsknin iyayensa da iyayenatun suna yar in barshi ya aureki yayi min alkawarizaiyi adalci a tsakanin mu kawai don ya ciro hannadaga cikin wahala ta dwo wajensa ba don yafisonta ba a kaina. Mahaifansa sunce in har naamince suma sun yarda ya aure mu mu 2. Nace har abada bazan taba amincewa ba. Hawaye ne yakezubowa daga idanuwan haisam yana rokonaamma naki fur.Ramlah ta sharbe hawaye tacigba da cewa.Bayan anyi hak haisam ya hkr akyi bikinmu ranardaurin aure ma haisam kuma yake ko. Bidiyo kasetan nuna babu abinda zaka gani a idanuwanhaisam sai hawaye, anyi biki an kaini gidana kowaya watse aka barni da haism. Babu binda haisam yake saidai y zauna a falo yayi shiru yan tunani saiinyi mgn sau gom haisam baya sanin binda nakecewa yana can yana tunani. Hira wannan ba mayida haisam balle zncen wata soyayya. Ina alkunyaina sharewa a matsayin na sabuwar amrya baikamata in dinga binsa shi namiji bai bini ba. To. In hour znyi sati ban shiga bangarens ba bazaizo indanake ba, gaisuwa ce kawai take hadani da haisam,bayan mun gaisa sai kllo da ido ko abinci na kaimasa baya ci sai dai ruwan shayi kwai yake sh, tunyan lekawa ofis wajen aikinsa kmfanin babansaanan yake aiki harm ya daina zuwa kwata kwata. Yaynsa habib yayi fdn har ya gaji ya kyale shiabokansa gaba 1 mgn suke meke damun hsam yacanja gaba 1 bay zuwa wajensu babu. Walwalabayason yin mgn ko sunje wajensa. Nim har wnnabu na haisam ya fara damuwa, inyi wanka inacaba ado amma haisam baisan nayi ba, is muyini a zaune haisam bai dago ki ya klli fuskata ba balle yaga jan baki da hodar dana shafa balle yaga fari daidon da nake yi masa da kallon soyayyar da nakeyimsa, in tkace miki. Munyi wta 4 cur da haisam. Hkko hnnu n bai taba rikewa ba blle ya shiga dakina.Is da abun ya isheni nayi yaji n tafi gidansu naje na sami mahaifiyrrsa na shaida mata halinda muke cikida haisam, ina kuka kamar xan mutu. T lallashenitace in daina kuk muka tafi gidan ni da ita mukasami haisam a zaune a flonsa. Kan kujerar dayasaba zama yayi tagumi. Yana tunani kamar ydda yasaba. Hjyr sa tayi masa fad sosai ta shada masa gara ya ski jikinsa ya dwo da walwalarsa zmansa danidram kuma har abada baza ta yarje masa yaje yaauro wata hanna ba. Bayn nan ne haism ya yardaya shiga daki na da daddare wani babban takaici.Ma muna kwance tre yana kirana da sunan hanna.Nayi fadan nayi fushin saidai ya bani hkr yace mantawa yayi gobe. Ma haka. Jikina ya fara sanyina fara sarewa na fara fitar da rai akan smunsoyayyar haisam yayi nisa sosai a fagen son hanna.Kullum sai ske dulmiya yke a tunanin hannah,baya cn abincin kirki ba'a hira dashi sidai gashi nanne kawi yana kano amma zuciyarsa tan babbanmutum garinku. Wasu lokutan da ymma yakn shigalambu yan busa wani dan karfe dogo kamr naazurfa da nayi bincke aka ce bun busrki ne akwai wsu tsakiyoyi. Akwatinsa suma wasu lokutn yandauko su ya baz a gdo da wani hoto tun. Kuna jjs 1ke da rauda kanwat da nusaiba haisam natsakiyarku shim ya kura ido yana kallo in takicemiki soyayya ta fr zautar da haisam ni kuma inagefe ina son maso wani, ni da dutse duk dya nake a cikin gidan. A haka muka shekara da hisam saimuyi wta 3 snn nake samu ya shiga dakina, tokoda ya shigo ma ba farnta min zaiyi ba dagakarshe sunan hanna zai dinga kirana. Nyi fad, nyiyji har na gaji haisan bay tnkamin balle ya bini bikoidan nayi yaji, da kaina nake zuw in dawo. Ban sami kulawar haisam ba, bbu soyayyarsa. Akwaiabinci , ga kudi da duk wani bu najin dadin duniyakatafaren gida, galla-gallan motoci duk waccenakeso it xn shiga. Mahifiyar haisam ce take yiminsutura. Ba'a yin wata gud is ta aiko min da dinkunahaka mahaifinsa ya budemin account. Banki yana turomin da kudi, yay hbib duk wata yake siyominkyn abinci komai da komai. Mahaifana knsu dakafarsu kudi suke bani suna kara rokona inci gabada hkrn zma da mjina tunda ni nace nji n gani inasonsa haka. Amma dukka gatn da surukaina sukeyimin da iyayena duk a banza ne ba dadin rywta nkeji b tund na rasa soyyyar mijina. Kowa ya rsakan haisam an rasa yadd za'a kamo bakin zrenbare a ware mana matsalar mu. Wani lkcmahaifiyata t kirani take shwarta ta ko zan hkr dawnn aure inzo in auri mai sona shima yaje ya aurowacce yakeso nace I ni ko da xan mutu gara inci gab da zama da haisam a haka sbd tsananin son danake yi masa.Haka nci gba da zam d hisam, kullum a cikintunani yake hour zuciyarsa ta samu matsala yakwanta ciwo likitoci suka ce lallai lallai haisam yancikin mtsananciyar damuwa ta tunani da kunci dolea dinga kwantar masa da hnkl don har zuciyrsa takamu da ciwo sbd damuw, bamu Da maganin wannan matsalar ta haisam sbd kece maganintsananin sonki shi yke damunsa. Don haka ciwonhaism yaci gaba da yaduwa kusan kullum a asibitihaisam yake daya ya dawo gida sai ciwo ya tashi amayar dashi asibiti haisam ya rame yayi duhu abintusayi. Wani abin mamaki a karkashin filonsa na asibiti abun busrki ne da tskiyoyinki yke ywo dasu.Likitoci sunyi sunyi da haisam ya rage damuwa sbdsamun lfyr zuciyrsa abu ya faskara. Akwai lkcn dahisam yayi wta 2 a kwanace premier clinic jikinbabu sauki saida aka mayar dashi aminu kanoteaching hospital amma in yanzu kaga haisam zaka dauka kafin ka fita bakin kofar dakin zi mutu sbdtsananin jin jiki da yake. Numfaninsa sama samadakyar abun tausayi,Hanna ta rushe da kuka gaba 1 wajen sai akafara hawaye, ramlah ma hawayen da take ya karakaruwa. Taci gaba da cewa nafi kow sanintakamaimai maye ke damun haisam ina ta zarginkaina nice silr wannan ciwon na haisam tunda nicena raba shi da abar kaunars. Da naga haka sai na yankewa kaina shawarar kawai in shiga gari dukinda hannah take inje in nemo wa haisam sbd itacekadai soyayyar da xan nunawa haisam amatsayina na mai tsananin sonsa banason in rrasashi gaba 1, gara na nemo msa maganin wannanciwo da yaki warkewa fiye da shekara 1 yana fama. Ban bari kowa ya sani ba, bn shawarci kowa ba nashirya tsaf da kayana da guzurina da direbana nashirya fita neman hanna, na yiwa surukaina daiyayena sallam akan zanje kd gidan wata kawatada mijinta ya rasu inyi mata ta'aziya kwana 2 kawizanyi, mahaifiyata ta nemi ta hanani tfy sbd ga jikin haisam yayi tsanani yana kwance a asibiti yaya za'yiince xanyi bulaguro duk da ma dai bani bace nakezaman jinyarsa kaninsaa ne izziddin damahaifiyarsa ai is suga ban damu dashi ba harkatama na tafi, nasan hakan data fada gsky ne baikamata in tafin ba amma nace ni dai zanje ba dadewa zanyi ba. Tayimin fatan Allah ya kiyayehanya sai na dawo na tafi.Kowa ya gyara zama dan yaji ci lbr cike da mmkda tausayin ramlah kowa ya zuba mata ido yanakllo musamman hanna. A zuciyata cewa tke waishin ko mafarki nake ne bad gaske bane ni ramlahta nemowa haisam, yi zanga haisam kenan? IkonAllah, Allah mai girma, Allah na gode maka, ko bazan auri haisam ba in ganshi ma nagode waAllah. Ramlah taci gaba da cewa "babban mutumgarinku na nufa na rasa gidan naku ma sai damuka yi tambaya don bn manta sunan mahaifinkiba mallam habu, nace yana da ya hanna wata farakamar da farko basu gane ki ba da hnne suka fi sanin ki ashe ko yar baba nace kece sannan akakaimu gidn naku she mahifinki ma ya rasu? Hannata gyada kai tace yafi shekaru 2 ma da rasuwa.Ramlah tace Allah ya jikansa. Mahaifiyar haisambabu abinda take iya cewa sai kuka kawai takeyikamar ranta zai fita mahaifiyar ramlah ce take rike da ita tana lallashi itam kuka take. Ramlah tace saimatar babanki muka iske take cemin suma basusan inda kike ba, kanin mahaifiyar yazo ya duke kitun bayan rasuwar mahaifinki kun tafi ksarsuniger. Na tambaya wani nigertace Dashi sunangarin muka kwana sannan muka nufi garin Dashi. Na dan sha wuya kfin nagano inda kike. Munyikwana 2. Gidan wni bawan Allah a grin muna yiwamatansa kwatance sai can daya daga cikin matantace hnna matr marigyi bello mdu custom. Nacemijinta ya rasu ne? Sukace ya rasu harta fita dagatkaba, naji dadi da sukace a ynxu baki da miji don zan iya tahowa dake, to amma yaya zanyi gashibaki sanni ba yan wanki da yanuwn mijinki ba zasubari in taho da ke ba, na tambaye su 'ya'yankinawa yanxu? Suka ce baki taba haihuwa b watankibakwai d aure mijinki ya rasu ya barki, sai kawai natuno wata dabara nace to tunda mijinki ya rasu bari ince daga gwamnatin jihar kano matar gwamna taaikoni don in kafa wata kungiya da za'a tallafawamatan da mazajensu suka rasu suka barsu damarayin 'ya'ya. Haka kuwa akayi nasa aka rakanifadar maigari Ni da direbana muka hada bkimukace tare aka turo mu. Dajin hak mi gri da jam'ar gari yasa akyi shela aka tar mana matan da mzansusuka rasu suka brsu. Kallo 1 nayimiki na gane. Ki,sbd na sanki a hotuna a wajen raudah kanwata tunkun aji 1 har aji 6. Tund nasan kin iya rubutusauran basu iya ba, nace to wacece tazo ta rubutasunan ta basu iya ba, nace to wacce ta iya tazo t ding rubutawa suka nun ku kika zo kika rubuta.Na babbaku taimakon da zn baku sannan nacetunda kin iya rubutu to ke zki dinga wakiltar sukina karbomusu taimako dga kano na nemi d kibiyoni kano, naci sa' kuwa 'yanuwanki sukaamince kika biyoni, don kawai in kawo ki wajen haisam.Wannan karon hann murmushi ne y kece matasbd tsananin farin ciki. Ta sake tattara hankalintawajen rmlh tana suaronta. Ramlah ta cigaba dahawaye tace hanna gaki a tsakiyar faalon gidanhaisam don kece kadai mganin da zaisa haisam yawarke daga wannan matsannancin ciwon zuciyar da yake fama dashi "ta sharbe hawaye tci gba dacewa Haisam ya sha wuy hanna a sanadiyyartsananin sonki, haisam ya rasa walwala a rywr sa asanadiyyr tsananin sonki. Haisam mi kaunar ki nefiye da duk wani mai sonki a duniya. Sai yu hnnataji amsar wnn klmomi data dde tan nemn dalilin da ke cewa haism yafi kowa sonta a duniya. Mahaifintane y fara fada mata, Bello madu ya fada mata haka,snn ramlh ta fad mata. Lallai na yarda haisam yafikowa sona. Hanna take fada a zuciyarta. Ramlah tasake rushewa da kuka mai tsanani tace ban barshikuma ya auri wacce yke so ba. Hanna ta matso na rungume ramlah tana lallashinta tana bata hjr itamakukan tkeyi, ramlah tace hanna dole nayi kukadole na dauwama a cikin bakin ciki har karrshenryw ta sbd halin wahala da bakin ciki dana jefahaism na cuceshi na cuci kaina. Hanna tce antyramlah daina cewa haka Allah ya rubuto sai anyi haka amma bake kikasa haka ta faru ba, ramlah tadago kalli hanna tace haisam ya sha wuya, kullumyan tunani kamar ya zautu don wni lokaci sai kagayayi murmushi yace hanna kenan tsananin tunaninki da yakeyi. Ni dai ina tare da GANGAR JIKINhaisam ne amma zuciyarsa na wajenki. Ramlah ta sake rushewa da kuka tce GANGAR JIKINSA NAAURA zuciyarsa na wajenki hanna. Ke kadai cemaganin ciwon nan na haisam hanna kece kawaizai gani ya warke.Hanna tasa hannu tana gogewa ramlah hawayecan cikin zuciyarta kuma cike take da farinciki datadade bataji irinsa ba cikin sanyin murya tace yanzuina yaya haisam din yake, ku kaini in ga jikin nasa.Gaba daya falon suka dauki kuka mai tsummazuciya. Hanna cike da mamakin meyasa suka sake rushewa da kuka kuma. Hnna ta dubi Ramlah tacelfy kuka sake rushewa da kuka? Ramlah ta dafakafadar hanna tace hanna saidai kiyi hkr Allahyayiwa haism rasuwa jiya yya habib yayo waya.Zasu taho d gawar a yau da daddare zasu iso.Hanna ta zabura ta mike tsaye yayin da zuciyarta ta far dukan 3 3 kanta ya fara sarawa kamar zai fasheta dora hannu aka yayin da jiri ya dauke ta ta komata zauna, ramlah ta riketa. Izzidin kanin haisam neya katse hanna daga tunanin da take ciki yazogabanta ya durkusa yana mai tsananin kuka dahawaye yace ni nake jinyarsa yace min duk ranar dana ganki na baki wannan. Ya mikowa hannatsakiyoyinta da abun busarta. Cikin snyin jiki tasaahnnu ta karba tana jujjuyawa ta gansu gr dasukamar yau ya karba daga wajenta. Sai ta tuno ranarda aka kai ta makaranta tan zaune akan akwati,haisam n kn benci yana mata tambayoyi har ya krbi wadnnn tsakiyoyin, sai hawye ya dinga digowadaga idanuwanta.izzidin ya ce bayan tfyr ramlahjikin yaya haisam ya rikice sosai har aman jiniyakeyi. Ashe yaya habib yana ta cuku cuku zai fitadashi turai. Bayan tafiyar ramlah da kwana 2 yayahabib ya tafi dashi londonRanar da suka isa da daddare Allah yayi ikonsayaya haisam ya rasu. Gingirim hanna ta tsaya tanakallon izzidin tamkar wata gunki. Izzidin yaci gabada cewa yaya habib yn kuka yayi waya yace yau dadaddare gashi nan zai juyo da gawar haisam shinewannan taron da kika gani ana jiran isowar su muke. Kiyi hkr hanna haka Allah ya rubuta miki.Haisam yasha wuya a sandiyar sonki. Kowa yayishiru ba abinda kakeji a falon sai sautin shesshekarkuka kowa keyi. Can hanna ta rushe da kuka tanacewa Innalillahi da inna ilaihir raji'un haka Allah yarubuta min haka Allah yaso ya ganni nagode wa Allah. Yanxu babu babana, babu mijina bello madu,babu haisam din da nake sa ran xan ganshi dukdaran dadewa. Hanna ta rusa kuka tana bada lbrnrywr ta tun ranar da mahaifinta ya kaita mkrnt sukagamu da haisam har izuwa aurenta da bello madu,har izuwa rana irin ta yau da aka bata lbrn mutuwar haisam. Tace ta dauka ita kadai kehaukarta Haisam yana can da matarsa ya manta daita tunda yace ya cika burin daya kudira akai nainyi karatu ya dawo gida yanzun zai cika alkawarindaya dauka. Sai na dauka haisam ya manta da watahanna ashe ina nan like a ransa. Hanna kuka wiwi Zaharaddeen Shomar Whatsapp 08168575100 GANGARJIKINSA NA AURA 2 Part 3 Posted by ANaM Dorayi on 04:41 PM, 30-Apr-15 Under: Gangarjikinsa ta Aura Jama'ar dake cike a falon iyayensa da iyayenramlah danginsa da dangin ramlah da makabtaduk sukaji tausayin hanna fiye da kansu da kansu.Hanna ke akayi wa mutuwa.inji mahaifiyar haisamyace min hjy ku barni na auri hanna, hjy hanna ceryw ta amma naki fur ashe kuwa da gaske yake gashi yanxun babu shi ina ma yana da rai yazoyaga hanna, sai duk falon aka dauki kuka gabadaya.Hanna ta kankame tsakiyoyinta da abun busarta acikin gyalenta ta mike ta dakyar tana hadahanya tana tafiya dakyar ta nufi wani daki ashedakin haisam ne, can lungu gado ta shige tayizauna yayin da idanunwanta suka fada kan wanikaton hoton haisam dake like a jikin bangon dakin yyi kyau sosai yana dariya a hoton. Taji gabanta yayanke ya fadi ta kurawa hoton ido kem yayin dataji wani ruwa dga hancinta yana zurara ta cikinkanta numfashin ta na kokarin dauke mata abundazata iya tunawa kenan , ashe suma tayi, Amratukanwar haisam aka turo dakin tazo taga wanni hali hanna take ciki karta nemi ta halaka kanta. Saikuwa tazo ta ganta ta jingine a lungun gado azaune ido babu baki sai fari ta kafe. Amratu takwalla ihu sai duk aka shigo aka tara hanna cikinwannan hali. Ba'ayi wata wata ba aka daukota anasalati aka yayyafa mata ruwa ta farfado.Tana bude ido taga dandazon jama'a har sunfina dazu mata da maza an idar da sallah magaribaan sake taruwa ana jiran isowar gawar haisam.Kofar gida cike yake taf da maza. Hanna tayi salatita tashi ta zauna tana tunanin a ina take ko daimafarkin ne, amma ta murtsike idon ta goge ruwan dake fuskrta taga zahiri ne ba mafarki bane haisamya rasu , ya rasu da gaske ne. Hanna taji sai sannuakeyi mata yayin da taji wasu na tambaya itacehanna? Wannan ce hanna? Wadanda suka zoyanzu kenan. Hanna tace a zuciyarta wato kowama ya sanni kenan kamar yadda nima acan duk wanda ya sanni yasan haisam,KARSHE Hanna ta matsa kusa da mahaifiyar haisam ta zaunasai taji mahaifiyr haisam tasa hnnu ta goge matahawaye, tace mata hanna yi hkr Allah ya kaddarahaka fatana ki din da yiwa Haisam addu'a kinji ko,Allah ya jikansa ya gafrta masa. Allah ya hadaki damai sonki fiye da gafrta masa. Allah ya hadki da mai sonki fiye da yadda haisam yake sonki. Hanna tagirgiza kai tace har abada ba'yi ba, baza ayi bakuma hjy, na rasa mai sona nima na rasa wandanakeso. Sai su duka suka rushe da kuka. Kanhanna akn cinyar mahaifiyr haisam tana kukakamar ta shiga cikinta don tsananin son da taji tana yi mata tamkar haisam tunda ita ta haifi haisam. Itamahaifiyar haisam ta dafa knta jin hanna taketamkar haisan ita tunda haisam na son hanna itamaharga Allah taji hanna ta shiga ranta. Amma aikingamaa ya gama haisan din daya hada ya tafi yabarsu, Can Hanna ta dago tace zanje inyi sallar mgariba?Hjy haisam tace eh jeki kiyi. Hanna ta mike dakyarga tsananin faduwar gaba da ciwon kai, ita kantabazata iya musulta yadda takeji a wannan rana ba.Ta shiga dakin ta kalli wajen da hoton haisam yakemanne taga an cire shi sai ta wuce ta shiga bandaki ta dauro alwalla tazo ta fara sallah. Bayan ta idar dasallar magariba ta tashi ta fara jero nafiloli sai tajigaba daya an dau salati tun daga yan kofar gidahar matan dake falo sai taji ana cewa sun iso, an isoda gawar. Tana tsaye tan sallah sai taji ta sulmuye tazauna kafarta ta kasa daukarta gbanta ya yanke ya fadi. Taji duk tsikar jikinta tana tashi, kukan da yakizuwa dazu ya kece mata tamkar ranta zai fita. Cantaji salatin da akeyi ya lafa sai ta rike bango ta tashitsaye dakyar don ta fita falon taje taga gawr abunkaunarta don idan taga fuskarsa yanzu ita ce kadaizata dinga tunawa har karshen rayuwarta. Duk dama taji a jikinta itama ba dadewa zata yi ba aduniya zata bi haisam dinta. Tunda damuwa datunani ne ya kashe haisam a shekara 2 ita yanzuyadda takeji ya linka yadda haisam yakeji don hakazuciyarta ta iya fashewa a wata 3 ta mutu ta huta.Tana tafiy a hankali don karta fadi.har ta fita daga dakin, tana fitowa taga gaba daya daruruwanmutanen da suke zazzaune a falon sun juyo sunakallonta gaba dayansu. Idonta ya dira akan watafuska wacce take tunanin ba gaskiya take gani bagizo ne. Kash!! Anan zan dakata mu hadu aGANGAR JIKINSA TA AURALittafi na 3 Naku ANaM Dorayi,Nagode da karfafamin gwiwan da kukeyi, Allah yabani ikon kammala 3 kamar yanda na kammala 1en 2...Bye! GANGARJIKINSA NA AURA 3 Part 1 Posted by ANaM Dorayi on 05:37 PM, 30-Apr-15 Under: Gangarjikinsa ta Aura Haisam ta gani zaune akan doguwar kujerardake falon, yaya habib a kusa dashi. Ta sake zareido tana kallon haisam taga dai shi dinne di hakataga shima yana murtsike ido yana kallonta yayindaya jawo hannun mahaifiyarsa yace hjy ga hannacan a mafarki ina ganinta. Mahaifiyarsa ta rushe da kuka tace Haisam ba mafarki kake yi ba hanna ce.Ya zabura zai mike da sauri yaya habib ya rikeshidon baya iya tashi tsaye, ya mayar dashi ya zaunar.Ramlah ce taje wajen hanna ta riko hannunta tanufo da ita wajen haisam. Tace haisam ga hanna,hanna ga haisam da gaske ne ba mafarki kukeyi ba, hanna ta rushe da kuka ta rungume ramlahtana cewa ramlah daman bada gaske kukeyi ba dakuka ce haisan ya mutu. Ashe zan sake ganinhaisam da idona? Hawaye ne yake zubuwa dagaidanuwan hanna da haisam. Yya habib ya nisa yaceikon Allah hanna yi hkr daina kukan yanzu duk jama'ar nan saurarona suke yi suji yay akayi akacemusu haism ya mutu kuma gashi yazo da ransa.Sami waje ku zauna hanna da ramlah suka smiwaje suka zauna babu abinda haisam yake saikallon hanna ko kiftawa baya yi itama kuma tamanta da a gaban jama'a take duk idansu kuma a kansu itama wani irin kallo takeyi masa mai daukeda tsantsar so da kauna. Mahaifin haisam da sauranjama'ar duk suma sun shigo.Yaya habib yace kamar yadda kowa ya sanihaisam na cikin tsananin ciwo muka bar kasar nanranga ranga muka tafi london. To mun isa cannayiwa asibitin da zamu kwanta waya suka aiko damotar asibiti aka daukemu muka tafi. Likitocin naganin yadda jikin yake baki da hanci jini sai suka ce zsu wuce dashi tiyata. Nasa hannu akan na aminceayi masa. Ina bugo waya ina sanarwa da bab dukhalin da ake ciki. Bayan sun gama masa tiyatar nesuka yi sukayi ya farfado yaki farfadowa suka smasa iskar kara numfashi (oxygen) don a jawolumfashin amma abu ya faskara sunyi iya kokrinsu na su nemo lumfashin sun kasa . To ni kuma danaga haka sai na rikice n bugowa baba way inakuka nace haisam ya rasu. Wani likita yayi yayikada in bugo waya harsai anyi wasu awanni a ganiko zi dwo sbd akawai alamar bi mutu ba, nace in aibbu surn wta ryw a jikin haisam. A take baba ya yiwa abokansa dake london waya akan suzosusameni. Asibiti suyi kokri a bamu gawar a gobe mujuyo gida nigeria ba sai anyi ta dogon bincikebahar kwana da kwanaki. Tunda ya rasu azo gida ayimsa sutura a binne. Abokan baba suka zo aka haudogon turanci likitoci sukace is an basu awa 12 suga ko zai farfado dnsu basu yarda ya mutu badoguwar suma ce in hour bayan 12hrs bai frfadoba to saisu bamu gawar.mun duka duk haukarsuce ta nasara mutuwa ai dy ce kuma kallo 1 zakayiwa haisam kasn ya mutu, ganin babu inda yakenumfswa da sukji tan dn harbawa shine suke s ran zai dawo ya rayu.Mun kirgaw hours da suka dibr mana sun cik submu gwar mu tho shine nayi waya nace gabanninmagariba yau zuwa isa'I zamu iso zo a taremu. Darana karfe 2 jirgi zai tashi daga london zuwanigeria haka kuma d krfe 2 awannin gom 12 zasucika da suka dibr man sai mu taho. Muka sayi akwtin saka gawa. N cike form din xan tafi dagawa. Karfe 2 na cika cikin ikon Allah akganumfashinsa ya fara dawowa. Likitoci sukyi sukyimu barshi suci gab da ceto rywr naga gr kawi mutaho tund di sunyi masa abunda zasu yi masashikenan sauran sai barwa Allah ikonsa. Tunda can gida nce ya mutu gar dai mu taho din idan ya rayuAlhamdulillahi idan kuwa ya mutu dam nce musuya mutu shikenan. Muka taho a hak sunan dai yanada rai wasu daga cikin jijiyoyinsa suna hrbawaamma ko motsi bayayi. Naga gara nayi shiru kdince bi mutu ba kafin mu karaso ya mutu gar ace kafin mu karaso ya farfado. Kuma cikin jirgin maakwai likitoci da sukaayi ta taimaka masa wajenjawo lumfashi. Cikin ikon Allah muna dira a garinkano ya fara numfasawa sosi. Mun sashi a cikinmota zuwa nan gidan ya bude ido yayi salati. Shineyanzu da yaga wannan taron jama'a yake tamby me akeyi, akace ai n dauka ka rasu shine 'yanjana'iza suka taru, shine yayi karfin halin ya tashizaune ya jingina.Farin ciki a zuciyar jama'ar bun ba zai misaltu bamusamman mahaifan haism da ramlh d hanna.Tamkar anyi musa lbishir da gidan aljanna.Alhamdulillh jama' ke cewa. Don da k ga haism andauko shi da idons kiri kiri yana kallon mutanewasu da yawa har sun fara rugawa a ztonsu sunga ftalwa. Wani abin kunya ma ba mata kawai ba harwasu mazan a kofar gida sun fara rugawa. Nan fakaji falo ya hargitse da kabbara da hamdala. Ana tataya mahaifin haisam da mahaifiyarsa murna dafatan Allah ya bashi lfy da tsawan kwana maiamfani. Murmushi kawai haisam keyi murna ta cika masa zuciya hk kawai ya tsine kansa yana mitsananin farin ciki badan rashin karfin jiki ba datsalle zaiyi ya taka raw don murna. Murna kuma itcega hanna yau gabansa, kus dashi tan kallons tanamasa murmushi,Zuciyar hanna kuwa tunda uwarta ta haifeta batataba jin frinciki irin na yu ba taji duk taa manta kunci da bakincikin datashishshiga ada. Tamkar ba'a taba mata rai ba aduniya balle tayi kuaka. Haisam ne yanxun wnnan a gabantabai mutu bashe? Kai Allah shine bin bautawa da gaskiya miryawa maikashewa mai yin duk yadda yaso d bawansa.Hanna take jinjinawa a ranta. Ramlah kamr tafi kowa farin ciki arantakasancewr hism bai mutu ba ta sanadiyyar jefa shicikinkuncin da tayi ta hana shi y auri wacce yakemutukar So, bayan haka bbu wani da namiji da take so fiyedashi a duniyahar yau. Ramlah na son hisam fiye da tunanin dukwandayasan soyayya. Wani babban malami ne ya rufe trod addu'a akan Allah ya kara baw haism lfy. Bayan n shafa neramlah tamike tace tana da magna ak bata izinin yinmaganarta. Byn tanemi gafarr haism da iyayen hisam da hanna daduk wasu 'yan uwans da suka fad halin tashin hnkali asanadiyyarwannan ciwo na haisam sai tazo gaban haisam tadurkusa tadubeshi tayi murmushi tace. Haisan ina neman wataalfarma a gareka idan Allah (S.W.A) ya baka lfy ina so k aurihanna sbda yanxu hanna bat da miji ni xan biya sdaki, lefe,kayan dakinamrya da duk hidiman da za'ayi a bikinku, nyikuskure ada dana hnaka aurin hanna yanzu na gane kuskure.Na. Haisamyyi wani lallausan murmushi ya gyada kai donbashi da karfinyin magna sai gaba daya aka dauki kabbara dukwajen, sai kowa y fra shiwa ramlah albarka musammanmahaifin haism.Hanna taji wani sanyi kamr knkara a ranta abunmamaki.Ramlah ta amince ta ura mata haisam da knta babuabinda takeyi a ranta sai. Godiya ga Allah wani sabon imaniyakutsuwa ranta ta ske gasgatawa kowaa yayitawakkali ga Allah,Allah zai ska masa ta wata hanyar da bai taba zatoba. Allah. Shine mai iko shine yake bayarwa a duk sanda yso.Mai hkuribay tbewa a snnu zaiga. Biyan bukta. Duk tsananikadak mntad ubangijinka yana sane da kai idan ka shigkuncishi ya kaaddara maka jarabawa ce don ya gwadaimaninka AllahuAkbar!!!Mahaifin ramlah ne ya rufe taro da addu'a yadinga shiwaramlh albarka da fatan alheri a rywr ta da fatanAllah ya basuzaman lfy ita da maigidanta da sabuwr abokiyarzamanta hanna. Jama'ar na amsawa da amin daga. Karsheaka shafa.Jama'a. Suka fara watsewa. Ramlah ta dukagabanmhaifiyrhaism tace hjy abar min haisam anan gidan nidahanna zamu cigaba da Kula dashi . Ko tantama mahaifiyarhaisam mabatayi ba ta ams da to. Shikenan. Don tasn barinhaism a kusada hanna babban. Maganin wannan ciwon nasa ne.Kowa ya tshi yanufi wajen motarsa. Don tfy gida, babu kowaa falondag haism sai ramlah a kusa dashi da hannah daamratukanwarsa 'yar kimanin shekaru 10 a kusaddahanna suna zaune a gefe. Ramlah ta fuskanci haism ya gji dazamanalamar yanasoya kwanta is tace bariin dauko makafilo adakika dan kwanta. Tamike ta nufi daki. Hanna tadago zata kalli haisam tag bbu abinda haisam yake saikallintatamkar yasami talabijin a gabansa ko. Kiftawa baya yi, tayimurmushitace yaya haisam sannu. Ya dan lumshe ido yagyada kai. Ramlah ce dauke da filo ta iso wajen da suke gamida yinsallama, Hanna ta amsa, Ramlah ta ajiye filon akan doguwarkujerar daHaisam ke kishingide ta kama shi ta gyara masakwanciya yakwanta sosai. Hanna ta yunkura ta tashi tana rikeda Hannun Amratu tace Anty Ramlah zamu shiga daki mukwanta wanedakin ne? Ramlah tayi murmushi tace haba Hannaaike babakuwa bace yanzu, duk dakin daya yayi mikishiga ki kwanta ai gidanki ne. Amratu tayi caraf tace Anty hanna zomujedakina mu kwanta zaki ga 'yar tsanata da AntyAamlah tasiyomin. Taja hannun Hanna suka tafi har sun juyaHanna ta juyo da kyakykyawar fuskarta ta kalli Ramlah daHaisam tayimurmushi tace sida safen ku. Sannan ta juya sukatafi.Haisam har daga kai yake don leken Hanna ganintayiyi tayi kyaun da duk a cikin kabilu kam daga bakar fatahar farar fataturawa da indiyawa bai taba ganin wacce tayi masakyaukamar hanna ba musmman a yu. Ramlah ta tsayakawai tana kallon Haisam taga kamar zaije ya jawo Hanna yarungumetakom ya hadiyeta yadda yake binta da kllo, sai tyi.Murmushi tadan taba hannunsa ya juyo ya kalleta tayi fari daido ta kanne daya tace Haisan ya akayi ne ko Hanna ta dawomuyi hira? Saiyayi. Murmushi ya. Koma y kwanta. Ramlah ta wucekicin donhado masa dan abu mai ruwa ruwa da zai iya sha.Bayan Hanna da Amratu sun shiga daki, Amratu ta nunuwahanna kayan wasanta da cartoons dintada littatafanmakaranta. Hanna tayi ta taya ta suna wasa da 'yartsanonintahar tsawon awa 1 bayan shigarsu sannan Hanna tace toAmratu ya isa haka jeki kiyi wanka ki daura alwalasallar isha'Iki fito nima zanyi wankan da alwalar. Dake akwaibandaki acikin dakin. Amratu ta fada bandaki bayan ta fito ne hanna tashiga. Tana wanka ramlah ta shigo dauke dasabuwar doguwarriga mai rubi 2 ta bawa amaratu ta ajiye mata kafinta fito,ramlah ta fito ta jawo musu kofa ta rufe. Hanna na fitowaAmratu ta mika mata sabuwar rigar barci dal a ledatace injianty Ramlah. Cike da fara'a hanna ta karbi rigarbccin ta sakasannan ta tayar da kabbarar salla isha'I . Har amratu ta gajida jiran hanna ta idr suyi. Kallon kset din cartoontaga saisalla take ta jerowa har barci ya dauketa hannabata idar ba,sai 3 dare snn hanna ta dar da nifiloli da addu'oin da takenagodiya ga Allah (S W A) da ya nuna mata wannanrana dafatan ubangiji Allah ya tabbatar da abnda ramlahtake shrinhadawa da fatan Allah ya bawa haism lfy.sai kuka ya kecemata don farin ciki. Ta hau gado kusa da amratutasa hannuta kashe fitila sannan ta kwanta. Wani laushi neyamutsu acikin tsokokin jikinta don bata taba kwanciya a irin wannanlallausar katifa ba tunda take. Sanyin na'urarsanyaya dakine(split AC) yake ratsa hudojin jikinta ta lumshe idosaita hangofuskar Haisam dauke da gwaza gwarzan idanuwansa yanakallonta. Bata dade ba bacci mai dadi ya sureta.Alarm dinagogo ne ya tasheta karfe 5 dai dai asuba tayi, tayifirgigit tabude ido taga fitila a kunne amratu harta shiga bandaki tanaalwalla. Hanna tayi murmushi tce a ranta birna saidan birniga kudi ga ilimi yarinya karama tasan ta saitaagogo ta farkada asuba tayi sallah. Bayan haanna da amratu sun idar da salla. Sai sukakomagado suka kwanta wani daddadan barci ya sakesuretangararai. Tayi firgigit ta tashi zaune taga rana harta ralle gari. Ta fada bndaki dan yin wanka ta dauki brushcikinjakarta daman ta taho dashi. Bandakin ma abinkallo ne awajen hanna taga komai na tangaran ne gamadubai duka kewaye da bandakin. Ruwan sanyi dana zafi ashaya dafanfuna abun gwaninban sha'awa. Abubuwadayawa saidihanna ta taba tabrshi sbd bata san amfaninsa babata gani baa. Aljannar duniya kenan gidan haisam kamar aturai. Dukinda aka zagya falo iri iri wajen cin abinci dakunamasugadaje na alfarma abin baya misaltuwa.Ramlah tayimutukar mamakin haism dubi yadda yaketsananin jinjiki amma sai taganshi daram kamar yawarke saidai rashin karfin jiki. Babban abinda yafi bataala'ajabi shinetunda take d haism bi tab tsyawa yan kallon fuskarta yna yimata murmushi ba is a yanxu data kawo masahanna har matace zata aura masa ita. Wannan abunda ramlahtaywa hsmyaji duk tsantar tsanar da yakeyiwa ramlah ta farakomawsoyayya kawai don ta fara son hanna. Haisam yajidukduniyar nan babu wanda ya taba masa kyauta maigirmakamar ramlah yaga babu abnda yake azabar so. Duk sandazai Kalli fuskar ramlah sai yaji sanyi yanzumaimakonhaushinta da yakeji ada. Ramlah ta fuskanci haknduk indatayi haism na binta da kallo yana murmushi. Haisam yajidadin wannan al'amari amma ramlah tafi jin dadikmr amafarki take ganin wadannan al'amari har haisamne yakedaga ido ya kalli fuskarta har yayi mata murmushi. Turkshi.,!..!!,!!! Kwanci tashi yau kwann hanna 6 a gidan haism daramlah. Akullum da safe hanna da amratu suna fitowa dagadakinsu suiske haism da ramlah a falo ko wani lkc ma. Daki suke samunsu, su shiga su gaishe su suyi masa ya jiki su komadakinsu.Duk lkcn cin abinci ramlah tan lekowa ta kira su, sufito suciabinci a dinning table, kuku 2 ne suke dafa abinci a Gidan,masu share share da goge goge daban. Don hakbbu aikin daramlah takeyi a gidn balle hanna ta tayata. Saidaisuyi wankasu zauna suna kallon satelite da kaset. Dinkuna masu kyau datsada ramlah tasa aka dinkwa hnna. Dnkunne dasark d zoben gwl rmlah ta baw hanna. A kwana shidan Nan itakantahanna tasn ta canja ta zma 'yar birni. Turarurruka kala kalaramlah ta sissiyo ta bata. Haism kuwa jikialhamdulillahi sukiyana samuwa yana tashi tsaye yana dan takwadaga daki zuwafalo inya haji ya zauna akan kujera a falo. Ranar da hanna tacika sati 1 da sassafe. Ta taashi ta fara harhadkayanta a jakana tafiya. Don taga ya kamta ta tafi gida kuma tunanamrmarinta kuma jikin haisam yayi suki gar ta tafi duk da bahakn take so ba.Bayan sun gama cin abincin safe ita da ramlh yuamratu tatafi mkrt tun 7:30am . Haisam daman ba abinciyake. Iya ci ba yna falons yana dan kurban shayi. Hanna ta dubiramlah tayimurmushita don sosa kai cikin ladani da alamar jin.Kunyatace anuty rmlah bbu abind zancemiki is godiyaAllah ya saka d alheri kuma Allah ya kara bawa yaya hasm lfy.Tunda nag.Jikin nasayayi sauki inaso zan koma gida yau karsuji shiru sufara tunanin ko b lfy ba. Ramlh tayimurmushi tacehar zaki tafi ki barmu, bako zaiyi halinsa kenan, ai ba laifikinyi kakritunda kinyi mana sta 1 mun gude. Akwi wasuatamfofi nas ansiyomin gasu cn a jaka na kum zuzzuba kudi aanbulun dubu 10 10 kowacce na rubuta sun ta. Bayn ambulundin daman inada jerin sunyenku saiki rrrbwa 'yan. Kungiyata inkinje. Hannata duka tayi godiya. Ramlh ta tashi ta shiga falohaism ta iske shi. Zaune kan doguwr kujera ya mikekaffunwansa akancentre table taje ta zauna a kusa dshi tan yimsmurmushi yadgo y dubeta yace uwr gida yaya akayi ne? Tayi farida ido tce ranka ya dade bakuwarmu ce takeso yau ta komagida tacekar hnkalinsu y tashi in sunji shirun yayi yawa.Haisam yajiwani dum a ransa b haka yaso ba yaso hnna tadade yana ganin ta yana jin dadi, can ya nisa yce har zatagudu ta barmubaza ta ske kwana 2 ba. Ramlh tace a'a gani nakegar tajeinyaso ta dwo daga baya kaga ni na daukota dagagrinsu karsu dauk guduw nyi da ita. Haism yayi murmushi yaceto shikenanAllah ya kaita gida lfy. Rmlh tace amin bari in kirat tashigotayi maka sallama. Ramlh ta tashi ta fito falo ta dubwajen cin abinci taga hanna bata nan is t nufi dakin amrtuinda sukekwana. A bakin kofa suka gamu hanna ta ratayojakarta zatfito. Ramlh tace oh! Hanna har kin fito lallai kno taishe ki Muna sonki. Ke kuma kina gudun mu. Hnna tayidariya tasunkuyar da kai kasa tace anty ramlah ba hakabane garinnamu ne da nisa shiyasa na fito da wuri don in isada wuri. Ramlah tace hakane to sai kizo ki yiwa haisamsallama ynn afalonsa,Hanna tace to,sai ta jiye jakar tana biye da ramlhhour zuwa falon hsm is ramlh ta fito ta barsu. Ta fitota nufi dkint yayin da zuciyarta ta hau dukn 3 3tana fargaba game da yadda tag kyau irn na hannamusmman yau da tayi ado da wta tsaleliyr shaddadata dinka mata combination ja da baki ga wannan lallausan gashin nn nata a tufke a bayanta. Zuciyarramlh nanuna mta hanna ta miki fintinkau a fgenkyau idan bkiyi d gske ba duk wannan iyakwalliyar taki da hour mutne suke yaba miki hnnazata zo ta fiki iyawa. Kalli yadda tayi wani kyu tmkar'year tsnr roba. Sai wata zuciyr tacewa ramlah rufw knki asiri ki kwantar da hnkl karki sa wnn a tnn maa zuciyark har wni tashin hnkl ya biyo baya yaddahaisam ya kwallafa rnsa da son hanna keme kikakwallafa sonsa a ranki to in kina so ki zuna klu kisami soyyyrsa to kiso hnna tunda gashi kin fr ganeknsa yan nuna miki soyayya . Hanna ta durkusa a gabnsa tace yaya inakwana, yaya jikinka? Yayinarai narai da ido yace hnna da sauki. Tashi. Dagann kizo nan kan kujera ki zauna. Hanna ta tashi tazauna a watakujera a gefensa. Kowannensuzuciyrsa cike da tsananin farin ciki is suka ji damakar su rabu su zauna dindindin suna ganin junnsu. Kallon kllo suke yiwa junansu na tsannin kaunajuna. Yayi murmushi yace hanna zaki tafi ki barnine, bayn ina ganinki inajin dadi ko bakya so injisauki d wurin kecefa kwayar magani da takekwntar min da ciwon. Hanna ta sunkuyar da ki tanajin kunyar bada wnn amsar. Yace yaya naji kinyi shiru ne? Hnna tace yaya dole ce tasa ba'ason rainanima xaan tafi in barka ba. Amma nayi mukaalkwarin kullum nyi salla zanyi maka addu'a Allahya sawke maka. Haisam ya gyada kai yace ngodeamma inaso ki min lkawaria rana zaki dinga tunanihar su 5, duk lkcn da kikazo yin sllaj zaki tunani kiyi min addu'a? Hann tayi dariya ina tunaka fiyedsau 50 a rana ba 5 bama koina ganinka,ko banaganin ka. Haisam ya gyara zama ya juyo yanakallon hnna yayiajiyarzuciya yace naji dadin duniyadazaki ring tunani su 50 a rana. Ynzu ki fadaminkalma daya da xan ringa tunaw a raina. Duk lkcn d tunaninki yayi min ywa sai ta kwantar min da hnkl.Hanna tayi shiru can ta dago tana murmushi ta kallihaisam suk had ido tag ya kura mata ido kawaiyana kallonta. Sai ta sake jin kunyarsa ta lullubefuskrta ta sake jawo gyalenta ta rufe ido ta miketsye. Hnkl ta nufi kofr fit tn tfy Hnkl. Haisam yce a'a tfy zkiyi ko sallama babu, kum aI baki bani amsarabinda na roka a wajenki ba. Hnn t juyo a hnkl takalle shi kallo irin wanda yke jinsa har tsakar kansatace abinda nakeso ka sa a ranka shineko daGANGAR JIKINa bata tare da kai Zuciyata tanawjenka. Haisam ya ske dagowa ya dubi hanna sai yaga ta daga mas gira tayi fri da ido tace kda kamanta soyayya gsky ce. Na tafi na barka lfy inakuma yi mk ftn kara samun lfy. Haisam ya kasa mgnsai kawai ya bita da kallo har ta daga labulan kofata fice. Ya rike baki yayi shiru jinsa yke tamkr ba'aduniya yke ba, kamar a aljanna aka jefashi yau gashi ga hanna a matsyin msoya masu shirin aurehar wadannan daddadan kalami suna fitowa dabakinta izuwa kunnuwansa. I can't belive this,hanna! Hanna ce kuwa.haisam yake fada a bainaye. Ramlah ce ta shigofalon ya dago ya kalleta fuskarsa cike da fara'afarinciki taf a zuciyarsa a yau, tace yallabai kungama sallama da hanna ko? Ga shehu direba ya fitoda mota zai kaita. Haisam yce munyi sallama dahanna ramlah sai dai ki bata kudin da zai isa tyi hidindinmunta. Anty ramlah. Ta dan harare shi suduka sukayi dariya tace kaima anty zaka cemin? Aina bata kudi ranka ya dade duk abinda ya kamatain bata na bata kada ka manta in so yayi so ra'ayiyana zuwa 1. Hisam yace kikace me? Tayimurmushi tace I feel wat u feel sbd ina sonka. Haisam yayi murmushi yace ramlah! Ramlah!!Ramlah tayi dariya snn ta fita. Ta raka hanna harbakin mota saida suka fita daga get snn ta dainadaga musu hannu. Haisam ne ta windon dakinsayake kallo hanna har suka tafi, yayin da wanikululun bakinciki na rabuwa da ita. Bayan tafiyar hanna da kimanin wata taji shiru ba ramlah bahaisam. Gashi babu waya a garinsu balle ta bugamusu taji lfyr su. Tun tana boye damuwarta akanhaka har hajr matar kawunta ta far fuskantrhalinda take ciki. A yau da yamma bayan hanna taidar da sallar la'asar sai ta shiga ta sallo wanka tazo ta hade dwani sabon dinkinta na materiak din daake yayi. Material din baki ne anyi masa kwalliya dajar fulawa.matsatsan dinkine akayi a rigar zanin ma anyimasa kwalliyar daya iri daya da yankar rigar. Hannata tufke gashinta da jan madauri (ribon) ta danadaurin dankwali mai kyau. Tasha hoda a fuskartada jagira snn ta sako sarka da dankunneta da zobena gwal da ramlah ta bata. Haka kawai yau da yamman nan taji tunanin haisam tayi mata yawashine take rayuwa a ranta shine tayiwa wnnkwalliya. Ta tsaya a gaban mudubi ta kalli kanta tajuya gefe ta sake juyawa baya taga lallai tayi kyausosai kamar ba ita ba dama yayi haisam na kusamana yaga wnn kwalliya da tayi. Ta fito tsakr gida wajen girki donta taya hajir aikin abincin dare dontaga hayaki n tashi tasan an hura wutar ita cenabincin dare. Tana fitowa hajir ta zabura ta mikekwalliy kika caba yau kamar mai shirin barin kasar?Kai gann irinta ba. Tasa hannun tana taba kayncikin hanna. Tce kai ai laushi garesu wannan ba atmfa bace.hanna tayi dariya tace ba tamfa bace sunansamaterial kinsan a wajen yn birni kaga abubuwa iriiri. Gunsu. Hajir tace lallai kuwa wnn matar ta cabaki da kyan alatu iri iri. Hanna ta nufi wajen garintuwo ta dauki rariya zata yi tankadae hajir ta rikerariyar tace hanna baza ki bata jikin ki da gari ba ga kayanki bakake barni kwai in karasa tuwonatunda har an gam miya na dora ruwn tuwo talgekwi zanyi in tuka na gama. Ga kujera can a gefe jekiki zauna dai muyi hira. Da rana maa ke kadai kikadafa abincin ni ina zaune ai yanzu sai ki huta ni inyi.Hanna tace ni ai zman hak kawai banaso sbd tun ina 'yar karama na saba da aiki barni kawai bakomai inyi miki tankaden. Haji taki fur suna tajayayya daga karshe hanna ta hkr ta koma gefe tazauna tana kallon hajir tana aiki. Hajir ta dago takalli hanna ce kwanan sai inga kamar kina yawandamuwa da tunani ko dai wani abu yna damun ki hanna? Hanna tayi murmushi tace babu abindayake damuna, hajir tace a'a fadi gsky ko sai na mikibaro baro ne, ai dole kiyi tunninsa haisammusamman kin baro shi ba shi da lfy. Su duka sukakyalkyale da dariya. Hanna tace donAllah ya akayikika ganeni? Da gaske abun ya fara damuna ni dai fatana ace lfyr sa kalau ba jikin bane ya dawo,hajira tace insha Allahu lfyr sa kalauita lfy ita kebuya. Amma lalle haisam ya samu shiga fiye dakowa har yafi marigayi samun waje. Hanna tayi drytace ni dai baza kiji a bakina ba. Hajir tace jiya kuwaahmad yake ce min a kalla masu sonki a garinnansun doshi mutane 5 da suka sameshi suka yi masa zancen don Allah ya basu izini suzo su nemiaurenki wai in sunzo wajen ki bakya fitowa. Hannata bude baki don mmk tace don Allah da gaskekike? Hajir tace wlh da gaske nake. Hanna ta gyarazma, ta dafe kirjinta tace me kawun yace musu?Hajir tace cewa yayi har a dangi an fara damunsa ya kamata kiyi aure g masu sonki ki zabi daya yacemin shi gsky bayason ki sake aure a kauyen nnyafison ki auri haisam. To amma gshi yau kusanwata 2 baizo ba bai aiko ba. In har ya bashi wasulokuta bai aiko ba zai shawarce ki, ki zabi wani tunda har akwai samarin da basu taba aure ba a wadanda suka sameshi da zancen suna sonki.Hanna tayi ajiyar zuciya tayi shiru tarasa ta cewa saitsnanin bugun da zuciyarta takeyi. Ta ce a ranta inhar haisam ya kara wata bai zo ba to nasan akwaimatsala. Ko ya hkr da sona ne? Kai haisam ba zaihkr da sona ba. Yaya xanyi yanxu in har kawu yazo ya sani a gaba yace in fitar da wani in aura?Sallamar kawu Ahmaed ce ta katsewa Hannatunanin da take yi. Ya shigo da saurainsa ya suritabarma sannan ya juyo ya kalli Hanna ya ce,"Kidauko gyalenki ki kawowa bak'i ruwa a sabonkwanon sha da kofina masu kyau. Hanna ta amsa da "To kawu."Ta juya suaka had'a ido da Hajir. Hajir ta ce "To koHaisam ne dan halak yak'i ambato ya iso garingabannin magariban nan." Hanna ta ce "Banjin ajikina ba, Haisam bazai zo yanzu ba.Ni har gabana yana fad'uwa Allah yasa dai ba masu neman auren nawa bane aka sami wanid'an.........ya canjawa kawu ra'ayi."Hajir ta ce "Kai haba dai tashi ki kai ruwan kiga kowaye." Dakyar Hanna ta mike saboda sanyun dajikinta yayi ta shiga d'aki ta yafo dan yalolongyalenta ja ta d'auko kwanon sha da kofuna 2 tazo wanke su tas ta cika da ruwan randa mai sanyi tanufi zaure.Kanta a sunkuye a k'asa tayi sallama ta ajiyekwanon sha a gaba bak'in sannan ta gaishesu batare data d'ago kai ta dubi fuskokinsu ba.Wata murya ce ta amsa mata gaisuwar kamar a mafarki muryar da take muradinta.Ta dago kai da sauri ta dubi mutumin sai tagaHaisam d'inta ne gefansa kawu Ahmed.Sai tayi murmushi ta sunkuyar da kai ta ce,"Sannu da zuwa yaya."Ta yunk'ura zata tashi ta shiga cikin gida sai kawu Ahmed ya ce "Hanna ki kawo ruwa a butoci guda 2don magriba ta kusa yi .Hanna ta amsa da "To kawu."Ta shiga gida.Ai kuwa da murna ta k'arasa wajen Hajir.Hajir na ganin yadda Hanna ke murna sai ta ce"Hanna ko dai addu'ar tawa ta ci, "Haisam ne yazo?"Hanna taje ta rik'e mata hannu ta ce "Hajir wlh shid'inne kuwa, ko mafarki nake yi ne?"Hajir ta ce "Gaske ne Hanna Allah sarki ya cikaalk'awarin yazo, daman kawun ki yafi sonki dashi.Daman ina jin jikin ne yahana shi zuwa Hanna ta ce "Kai gaskiya babu alamar jinya a tare dashi yayi fariya murmure daga ramar da yayi kinga k'ibar dayayi kuwa, baza kice ya ta6a yin wani ciwo har anfasa masa kukan mutuwa ba."Hajir ta ce don Allah?"Hanna ta ce "Ai yau duk kunyarki sai kin lek'a kin gaisa da mijina."Su duka suka tuntsire da dry.Hajir ta ce,"Hanna ko 'yar kunyar nan babuwannan karan lallai anayi da Haisam, ai kuwazanzo mu gaisa."Hanna ta wuce ta d'ibo butoci ta wanke su tas ta ciko su da ruwa ta nufo zauren da suke zaune.Daf da ta shiga zauren taji Haisam na cewa "Zanyitafiya zan dauki kimaninin watanni 2 a turai ammaina neman izini zan turo magabatana su zo nemanauren Hanna.Ina fatan dai Hanna ta gabadar dani a wajenku daman ko?"Kawu Ahmed ya gyad'a kai ya ce "Kwarai kuwa tunsanda naje Nigeria zan daukota tun daga can tafara bani labarinka.Kai ka dauki dawainiyar karatunta harta gamasakandire. Sannan data dawo daga Kano, tafiyar nan ta kwanannan ta fad'amin kakaf yadda aka yi.Allah ya saka da alheri.Haka Allah ya k'addaro muku shine yake yin yaddayaso da bawansa.Babu komai ka aiko magabatanka ai ba sai an yiwani dogon bincike ba ai kunsan juna tuntuni. "Hanna tayi sallma ta shigo zaure ta ajiye butocin agefe kanta a sunkuye a k'asa ta koma cikin gida. Bayan sunyi alwala, masallacin dake kofar gidansuka shiga suka yi salla tare da jama'a.Hanna ,ma anan cikin gida tayi salla bayan ta idartasake rangad'a kwalliya a fuskarta ta gyarad'aurin d'ankwali.Ta sami waje ta zauna tana jiran akirata taje ta gana da abin kaunarata.Amma abu d'aya daya tsaya mata a rai takenanatawa da Haisam ya ce zai tafi turai sai bayanwata 2 kafin ta sake ganinsa.Son Haisam ya sake yad'uwa a zuciyarta fiye danada a kullum yana lkie a zuciyarta ko sakon daya bata iya yi ba tare da tayi tunaninsa ba.Kawu Ahmed ne ya shigo ya ce"Hanna zaki iyazuwa ku gaisa shi kad'ai ne a zaure ki kunna fitalarkwai don zauren da duhu.Ya ce a yau zasu koma Kano ba zai kwana ba nikuma zanje wajen baba Sha'aibu in fara sanar masa da zancen aurenku."Hanna ta amsa da "To kawu."Kawu Ahmed ya fita.Ta mik'e ta shiga d'aki ta d'auko fitila ta nufi zauretana takawa d'ai-d'ai tana rangwad'.Tayi sallama ta ajiye fitila a gefe.Haisam ya d'ago kai da sauri yana kallonta hartashige lungu can gefe ta takure ta tsugunna sannancikin ladabi ta gaishe shi.Yayi murmushi ya amsa mata.Ya ce Hanna kamar zan gudu dake kika tafi can nesa kika takure, ganan gefen tabarma kusa danizo ki zauna mana.Koda yake Hanna kin manta da uncle Haisam tunwata shekara ko?"Hanna taji dariya ta kubce mata, Haisam ma yayidry. Hanna ta taso tazo gefensa ta zauna.Ta d'aga ta dubeshi suka had'a ido yayin da watakibiyar SO ta caccaku a zuciyoyinsu.Hanna ta lankwashe murya ta ce "Yaya jikinka?"Ya k'ura mata ido can ya ce "Ai tun ranar da nahad'a ido dake na nemi ciwon na rasa, kuma tun ranar da nace miki good bye na tafi na fara ciwo."Hanna tayi murmushi ta sunkuyar da kai k'asa tace,"Ina fatan har abada zan dauwama a wannanmatsayin daka bani."Mamaki ya kama Haisam ya ce a ransa "Hanna ce take fad'a min haka ko mafarki nake, a zatona sainasha bak'ar wuya da Hanna kafin ta fara sona saikuma nayi da gaske kafin ta waye da irin wannansoyayyar ta 'yan birni.Ashe ni Hanna a waye take harta wuce tunanina.Ga iya kwalliya cas kamar 'yan birni, ga wani kallo da take yimin ko wata 'yar birnin me digiri bataiyaba."Hanna ta katse masa tunaninsa ta ce "Naga andoshi wata 2 bn ganka ba sai na shiga fargabarkoda ciwom ne ya dawo maka?"Haisam ya ce ciwo ya tafi kenan insha Allahu tunda Allah ya kawo min maganinsa.Hjy ce dai ta hanani zuwa wai a rame nake tafi sonin zo miki da k'ibata.Zaki fi murnar ganina wai."Hanna tayi dry. Hakasuka shafe fiye da auwa 1 suna hirar so da k'aunakowa na fad'ar kalmar da zata dad'ad'awa d'anuwansa.Yau jinsu suke kamar a aljanna suke, d'an zaman nan da suka yi.Daga k'arshe Haisam ya shaida mata cewa zasu tafiNew york jibi shi da Ramlah zasu had'o kayanlefenta kuma Ramlah ta ce ace mata itama honeymoon d'inta ne wannan fitar don tunda suka yiaure ko Abuja basu ta6a zuwa tare ba kafin amarya tazo itama taje nata.Hanna ta yi murmushi ta ce "To Allah ya kiyayehanya.Ya dawo da ku lafiya.""Haisam ya ce abunda zaki ce kenan?"Hanna ta ce "Me zance wanda yafi wannan?" Haisam ya ce "Kice asha honey moon a had'ominlaefe mai kyau.Kuma incewa Ramlah in Allah ya yarda kema zakozo ki fata da angonki Honey moon lafiya."Hanna tayi dariya ta rufe ido ta ce "A'a,"Yaya Haisam ka rufa min asiri karka fad'a mata haka ni na isa in fad'awa aunty na haka?"Haisam ya ce"To meye Ramlah k'anwa da k'awa tad'aukeki.Bata da wata hira da ta wuce tayi min hirarki shiyasa nake jin dad'in hira da ita yanzu."Hanna tayi shiru tana tuno yadda Bello Madu yake yi mata.Hak'ik'a Ramlah tayi dabara a sannu zata samu Syya wajen mijinta kamar yadda Bello Madu ya farasamun shiga a wajena sbd kawai yana yi min hirarHaisam. Haisam ya mik'o mata wata k'atuwar abulan tadahannu 2 ta kar6a ya ce "Inji Ramlah ki rabawa 'yank'ungiyarku tunda kece shugabar k'ungiya ashe.."Hanna tayi dry ta ce "Ashe ka sani wa ya gayamaka?"Ya ce "Ramlah ta bani lbrn yadda kuka yi kakaf." Ya miko mata wata k'atuwar leda ya ce wannannakine inji Ramlah."Ya mik'o mata kwalin wata waya mai tsada ya ce"Wannan wayar tafi da gidan kace zaki gadirections d'inta a jiki da charje in an kawo wuta kidinga sawa caji. Hanna tayi kasak'e tana kallonsa tana tunanin yaza'a yi ya bata waya a k'auye nan bayan babuservice a garin.Haisam ya gane abun da ya d'aurewa Hanna kai saiya ce "Wannan wayar #THURAYA ce tana yi a wajen da babu service dan haka duk sanda na bugo mikiin dai da caji kuma a kunne take zan sameki inafatan duk kin san yadda zaki yi?"Hanna ta ce,"Na sani Yaya."Ai satin dana yi a Kano Amratu ta nunamin a tata. " Kud'i ne a shak'e a cikin wata yar jaka ya mik'amata ya ce "Dollar America ce wannan sbd bani dakud'in Nijer amma dalla za'a iya canja ta a ko ina,kin dinga kashewa.Ki bawa kawunki duk yadda kika ga dama a cikinkudin. Kada ku sake ku sayi ko cokalin cin abincina aure.Sabon gida nake gina muku mai bangare 2 naki dana Ramlah yadda kowa da bangarensa a sati ma wani ba zaiga wani ba. Idan kuwa kika bari sukasuyo miki wani abu to asararsa za'ayi." Turawa nesuke gina gidan, haka su zasu zuba kayan ciki irinna kalar data dace.Bana son abinda za'ayi asarasrsa kinji.Farin ciki mai had'e da mamaki ya rufe zuciyar Hanna ta tsaya kawai tana kallon Haisam.Can tayi a jiyar zuciya ta ce "Yaya naga gidan nakuma mai tsananin kyau ne kuma sabo gashi dagirma me yasa zaka sake gina wani?"Yayi murmushi ya ce "Haka Ramlah ta ce itama inhad'a ku kada in warewa kowacce 6angarenta ni dai a tsarina da ra'ayina naga gara in bawakowacce 6angarenta.Kuma kinsan ko harshe da hakori ma ana sa6awani kuma gani bani da hkr idan naga za'a ta6a min'yar k'anwata Hanna, ina tsoratarwa da cewa zaniya kashe duk mai shirin jefata a cikin tashin hankali a rayuwarta." Suka kyalkyale da dariyagaba d'ayansu,Haisam ya mik'e tsaye da dariya shirin tafiya, Hannata durk'usa gwiwoyinta a k'asa ta ce "Yaya na godemadallah Allah ya saka da alheri.Sai ta fara hawaye shar daga idanuwanta ya ce a'aHanna kukan mi keki yi ne? Kada fa in kasa tafiya in naga kina kuka."Ya sa hannu a aljihu ya ciro wani farin hankaci yamik'a mata ya ce ta goge fuskarta kuma baya songanin hawaye a fuskarta.Ta taso tana rakashi yana mata hira mai dad'i akanta kwantar da hankalinta ba zai iya kaiwa tawa 2n bama zata ganshi ya dawo.Kuma ko da basa tare zuciyarsa na gareta.Direban da ya kawo Ramlah shine ashe ya kawoHaisam.Hanna ta ce "A'a tare kuke kak'i shigowa kasha koruwa ma." Shehu ya ce ba komai suna da ruwa a mota."Ya durk'usa har k'asa ya gaishe da Hanna.Taga abincin gwangwani iri-iri da lemongwangwanaye ga robobin ruwan swan nan a cikinmotyar sai taja bakinta ta yi shiru.Don har da zata ce sai sun tsaya sunci tuwo. Taga masu irin wannan dauka ya za'a yi su ci iya cintuwonsu miyar kuka lami sai wake aka watsa a ciki.Haisam ya ce da direbn ya bud'e but ya shigar dakwalayen da suke but din cikin zaure.Kwalayene manya-manya guda 3, mak'il suke dakifin gwangwanaye da biskit da alawoyi k'arama cikinsu kuma cike yake da kayan shafe-shafe nakwalliyar 'yan mata.Hoda,janbaki,mayukan shafawa,a jiki dana, gashi dana hannu.Daman Haisam mai son irin wad'anan abubuwanneshiyasa ya siya mata mayukan gyara ta sake yin fes.Ga turarurka designers abun baya misaltuwatsaddadu.hanna ta langwabar da kai, ta rike murfinmotar.haisam kuma na zaune a cikin motr gidngaba. Yayin da shehu direba ya tsaye can kofargida yana jira su kare sallamar. Ta yiwa haisamwani luguiguitaccen kallo cikin muryar sanyoyyiytace yaya haism nagode. Bansan wacce kalma zanyi amfani da ita ba wajen nuna maka godiytaba, tun ina karama kake fama dani har yau bakadaina ba ubangiji Allah ya saka maka da alherins.Yace kina bata bakinki wajen gode min balle hrkiding tnn kalmar da zaki yi amfani wajen nuna mungodiyarki. Ni. Tnn na duk abinda nayi miki dole ne a wajena ba sai kin gode mun baki duaka aikina neai dole inyi miki. Hanna tayi dariya tace haba yaya nina fara saka haka a zuciyrta na gode dai znce. Dagakarshe suka yi sallam akan zai bugo mata waya.Yana. Tsokanarta wai yaga duk ta rame ko batasonaurensa ne, za'ayi mata auren dole. Hanna ta kasa bashi amsar wnn tambayar ta bishi da kllo direbayaja motor suka tafi. Yana dago mata hnnu itamatana daga masa. Bata shiga gida ba saida ta dainahango fitilar motrsu. Kawu Ahmd da matars har sunfi hanna mmk datsananin farinciki wnn kyaututtukn na haism damatarsa. Raba dare sukayi kawai suna kallondukiya suna sambatu. Hanna kuma ta shaida masucewr yace bai yarda a siya mata ko cokali ba nakayan daki shi zaiyi komai. Nan kawu ahmad ya sake jin wani sabon farin ciki ya lullube shi. Saiwajen 12 dare snn hanna da kawunta da matarsasuka shiga dakunansu don su kwanta. Hanna tashiga nata dakin ta jawo kofa ta bame is kuwa tadauko kwalin wayarta ta fara karanta yanda akeamfani da ita. Abunka da nasara ya rubuta dalla dalla yadda ake amfani da ita in hour ka iya karantaturanci zaka fahimt nan take karfe 1 daidai akakawo wutar lantarki. Hanna ta mike daga kankatifrta taje ta jona caja a soket ta jona wayar sainan da nan taga wayar ta fara caji. Murna ta rufenata tnn haisam. Taga da wnn kwanciyar da take tana ta tunnin gara ta tashi tayi 'yan nafilfili ta godewaAllah da ya bata abin data dade tana nema. Bayan tfyr hiasam da kwana 4. Hanna na kwance adkinta misaln karfe 11 na dare taji wayarta ta hukara ta zabura tatashi zaune ta jwo wayar tanakallo taji dai bata daina karar ba. sai tace a ranta kohaisam ne yake kira. Ta jawo kwalin wayar da saurita sake karanta wayar dai ringing take ana sake redialing. hanna ta danna wajen daya kamata tadanna don amsawa. Sai ta kara kunneta ba taredata ce komai ba. Murya tji anacewa hello hanna,hanna,ko ba hanna bace? Haisam ta kyalkyale dadariya tace yaya haisam kaine? Haisam yayi dariyayce bkyauyiya ashe kina jin tsoron kiyi magana. Hanna ta gaishe shi tace kwana 2 shiru banji kayiwaya ba kullum da ita nake kwana a kusa dani waiko zaka kira cikin dre. Haism ya ce oh I am verusorry tun shekaranhiya ban zauna b ina zurgazurga a airport jiya kum a jirgi muka kwana. Hannatace har kunyi tfyr. Yace yanzuma muna london ni da ramlah. Hanna tace lah yaya ina anty ramlahtake mu gaisa. Haisam yace ramlah ta fita kasuwakinasan da daddare aka fi yin hindindimu a turai dakasashen larabawa. Hanna lefen mu fa ramlah tatafi suyowa lefan auran haisam da hanna fa. Hannatyi dariya ta rungume filo haisam ya kashe murya yace banji kince komai ba hanna ko damn aurendole za'yimikibakya sona? Tayi fari taya mutse fusktace cewa zak yi ko na daina sonka ne. Bawai kobana sonka ba, tunda kasan ina......., sai tayi shiru.Yace yaya kika yishiru, da kina me? Hanna tace to aishikenn a bar maganar. Haisam yace ai sai kin karasa so nake daman ki fadi wannan kalmarshiysa na tsokano zancen kina me? Hanna tce toyanxu diso kake inyi rashin kunya yaya da kunyaince ina...... Ta sake yin shiru bata karasa ba haismyayi murmushi yace hnna kenan aure fa zamuyiyaya za'yi ure d kunya ai da kin dan fra rarrageta kafin in fizget gaba daya in yasr. To nibariin fadmikiabinda nakeso ki fadaminkika kasa fad. Hanna inasonki. Taji wani abu ya disa a ranta, dadi yalullubeta tyi ruf d ciki akan katifarta ta dora kantaakan filo tana sauraron daddar muryasa, tayi shirubata amsa ba yace hanna ko bakya jina ? Cikin shagwaba da kashe murya tace yaya ina jinkashirun da nayi wani abune ya disu a zuciyata yakezagayawa a kwalkwalwata nake kokarin warwareabunda yake kokarin ya cushe min. Y lumsheidoycekmryaya fa? Ta nisa tace ina cikin watamatsannanciyar soyayya wacce ta zame min ciwo a raina na fara zama mutum mutumi, gangar jikin nwani wajen zuciyata kuma tan wani waje. A kullumkum koda yaushe ina sake saken wasikar jakiidnin ido 2 a bacci kuma ina mafarkan da nakedukarsu tamkar tatsuniya. Sai gashi a yautatsuniyta tafara zama gsky. Shine nke tnn shin a mafrki nake jinka ko kuma a ido 2? Haism yayimurmushi ya ringinsa akn kujerar shakatawa dayke a bakin swimming pool din wani katafarenhotel da suka sauka a london.yace hnn this is rel,not dream so our dreams come true. I love you, ofcourse I do. You mean much to me hanna. I missed you so much........kfin haisam ya rufe bkins is yjimuryar hanna kamr daga sama cikin sanyayyiyarmurya tace yayahism na soka, in sonka fiye datunanink fite da duk wani mutum a duniya. I loveso much. Ya gyara zama yace hanna ya fiye datshon mijinki daya rasu, haba hanna kodai don king ya rasu ne? Su duk suka kyakyale dadariyahanna tama rasu irin amsa da zata bashi.Haka hanna d hiasam suka ksnce sun hira mai ddihar karfe 2 dare snn suka yi sallam sukaa aajiyewaya. Kowannensu juyi kwai yakeyi a kwance donmurna bata barsu suniya barci ba.kullum hak haism yake sai ya tabbatar hnna ita kadai ce shimshi kadai sai ya bug mta way su kashewa junansuzuciya. Bayan tfyr haisam da sati 3 'yanuwan haisam mzasukazo neman auren hnn suka bada kudin komaida komi sdki ne da lefe kwi suka rage b'a bayar ba.Murn wajen hnna da haism abin baya misaltuwa.Watan su haisam 1 da sti 2 da tfyrsu snn suka dwo.Cikin ikon Allah sai ga rmlah tayo tsrbr ciki, kowa murna yke musmmn iyyen hism suna jin ddin yaddrywr haisam ta far gudana kmr ta kowa. Duk indaka ganshi fara'a yake wasa da dariya d mutanekamr yadda yake ada. Ga wata uwar kiba da yakeyi da fari baza kace wnn kshi da ran bane. Ramlahma kamar tfi haism smun cnji a rywr ta sbd itama mafarkinta ya zama gsky. Tana samun kulawarhaism sun zma suyi hir, suci abinci tare su kwantagado dya. In tayi kwalliya ya Daga ido ya kalletayace tayi kyau. Wnn ba karamin canji ramlah tasamu ba. Mai hkr yakan dafa dutse yasha romon sainji bahaushe.Bayan su haisam sun dawo da kwana 3 danginhaisam mata suka cika hadaddun motocinsu naalfarma suka nufi Dashi garin su hanna da lefe dasadaki. Daman hanna ta sanarwa da kawun taranar da zasu zo dan haka suma suka hadawa bakiabinci da abin sha irin nasu na 'yan hutu. Harda mahaifiyar Ramlah akazo da danginta wasu kwaidan suga Hanna suka zo.cikin rashin sa'a basusami ganin Hanna ba don tun 7 na safe Hanna tagudu ta tafi can garin magarya gidan watatsohuwar kakarta ta buya don kunyar surukantatakeji. Dangin Hanna sai suka zama baki bude dontsananin mmk ganin yawan lefen hanna tundasuke basu taba ganin irin akwatinan nan ba ballekayan dake ciki. Wasu rundima rundiman akwatinane masu santsi har guda 6 bi da bi ta kashensu'yarkit ce a dankare take da gwala gwalai da fashions mai tsada irin na turawa. Leshina da shaddoji dakyana tsukewa abun bazai misaltu ba takalmada jakunkuna hadaddu mayuka kuwa turarruka basai na zaiyana ba daman can ya siyo mata balleyanzu akwatinsu suma daban. Iya haule surukartana wajen karbar lefe hanna sai ta zama abun kallo wasu kuma ta zamar musu abun dariya gaba dayasaita rikice ta hau surutai. Ita abun ya zamar matakamar wani rufa ido yanzu duk wannan kayn nahanna ne, yanxu hanna ta dage ta tafi ta barta tayikudi kenan bza ta iya ganinta ba balle ta sata aiki.Allah kenan haka yake yin ikonsa ansa ranardaurin aure sati 2 kacal sukace kuma a ranar sukeso a zo a tafi da amarya ba sai an bata lkc ba. Damnsun taho da kudin sadakisu d kudin dinki duk.Msuka bayar, makudn kudi suka jifgewa danginhanna a gabansu, wasu suka dau kukan murna wasu suka rafsa buda suna kirari. Dangin haisamsunji dadin yadda aka karbe su a garin suhnna.kmar za'a hadiyesu ana ta yi musu marhabanda wasa da dariya suka rabu akan nan da sti 2 zasudwo su tafi da amaryar su...............JUMA'AT KAREEM**GANGARJIKINSA TA AURA 3** =============9⃣=============RANAR DAURIN AURE Ranar jumu' a ne ranar daurin auren haisam dahanna da misalin karfe 2 na rana za'a daura aurenbayan sallar jumu'a. Garin dashi ya cika makil dajama'a taron da ba'a taba yin irinsa ba a garin.Manya manyan masu kudin kano sun halarcidaurin auren haisam, abokan babansa da 'yanuwansa abun sai wanda ya gani hardagwamnan kano na wnn lkcn ya halarci wnn daurinauren. Dangin hanna na nesa danakusa sunhallara, 'yan garin kuwa da wadanda aka gaiyatada 'yan gaiyar sodi duk sunzo su ganewaidanuwansu kar suji ana fada su basu ganiba. Babu abinda zaka dinga hangowa a garin sai wasu jifgajifgan motoci bakake masu bakin gilashi sai kumafararen shaddoji da tsadaddun ya dika a jikinmanyan masu kudin da suka halarci daurin auren.Kamshin turare har cikin gidajen 'yan garin 'yanjaridu tududu na nan nig daniger suna ta daukar a hoto da bidiyo kaset. Ga mahaifin haisam danaramlah a kewaye da jama'a. Hiasam kuwa kohangoshi ma baza ka iya yiba sbd jama'a kowa soyake ya gaisa dashi kowa yana so haisam yaganshi yasan yazo donduk dangartakarka dahaisam yace zaku bata in har baka zo masa wnn daurin auren ba. Kafin karfe 4 har an shafafariha andaura auren haisam yazama mijin hanna. Allahyabada zaman lfy. 'Yan daurin aure mza sun farashiga motocinsu masu babura da kekuna sumasun fara shiga motocinsu masubabura da kekunasuma sun fara hawa sunakama gabansu anci, ansha lemunan gwangwani da ruwan kwalba kudiaka dinga rabawa a wajen daurin auren, hakaango ya dinga danko kudi yana rabawa mutanedon murnarda yake ciki a ranar saida babansa yace ya isa haka snn ya daina . Maroka duk sun cikaaljihunsu da kudi da goro da lewa ga ruwan sanyi sun jika makoshin su. Kowa yana san albarka dafatan zaman lfy ango da amarya.bayan maza sun watse motocin da zasu daukiamarya da kawayenta da 'yanuwanta don rakatagidan mijinta suka karaso kofar gidansu hannacikin gidan maki yake da mata ko hanna bakahangowa mai bidiyo kaset da kyar ya nemoamarya ya haskata. hanna ta caba ado da wani rantsatsan lashi baki mai adon rawayar fulawa ta sagoggoro rawaya takalmi da jakarta baki. fararenhannayenta da kafafunwanta sunsha fulawar lalle.kirjinta ta da kunnuwanta da hannayenta dambaradambara gwala gwalai ne. babu abinda zakaji idanka matso kusa da hanna sai kamshin turaren wuta don ta tsuma da (dukan) tun na saura wata gudaauren kakarta ta dinga tsumata ciki da wajeabunka da azbinawa sunsan sirrin shirya amaryatayi tsaf ciki da bai. an dilke fatar hanna angurgetada kayan gyara jiki tayi sumul sumul ta kara jawur.abunka da farare jawur jawur zaka dinga hangowa cikin gidan gashi yalalo yalalo har bata danginhanna dai dai ne bakake duk jajaye ne.Motar da za'a dauki amarya tafi kowacce girma dakyau.Hanna ta shiga ita da Hajir matar kawunta dasauran sa'aninta 'yan uwanta dan ita bata dak'awaye 'yan uwanta ne k'awayenta.Tsofaffi suka dinga duruwa sauran motocin kana shiga sai kaji wani sanyi ya daki hancinka A.C ce tagauraye motocin.Hatta manya-manyan bus din da aka turo masu A.Cne da labulaye a wandunnan. Duk yawan motocinda Haisam ya turo sai da wasu suka rada waje saboda yawan jama'ar da suke so suje Kano sugagidan Amarya.Motocin suka fara tafiya sai Hanna ta kece da kukatana d'agowa mutane maza da mata hannu.Har aka iso Kano Hanna kuka take su Hajir sunalallashinta tayi shiru. Can ta tuna da mahaifinta dama ace yana da rai mana wannan dauka da tazomata data taimaka masa, haka yayi rayuwarsa haryamutu a cikin taulaci sai kuka ya kece mata.Sai da magagriba suka isa gidan amarya a wataunguwar jiga-jigan masu kud'in Kano gidan Hannayake mai suna Nasawara G.R.A. Rigiji gafjin Haisam ya tsantama gida duk layin babugida mai girma irn na Haisam da kyau.Aka wangame jifgegen get din gidan motocin duksuka shigo farfajiyar gidan, amma duk da haka gafili nan fetal wasu motocin ma fiye da biyar zasu iyashigowa ciki sbd filin farfajiyar gifan babbane. Fulawoyi ne a shuke a jikin katangar gidan gatsuntsaye nan da d'awisu da talo-talo a zube afarfajiyar gidan suna ta shawagi.Sanyi k'alau ciki sbd wasu zagayayyun dawatsuaka gina masu 6uldulo da ruwa yana tashi sama.Kasan da ake takawa abun a kalla ne balle cikin gidan.Gidan 6angaren 2 ne iri d'aya ga wani dank'arerengida a tsakiyarsu. Sai aka nuna musu gidan Hannana gefen dama suka d'uru ciki,wai! wai!! wai!!!Ai suna shiga sai suka ga ashe basu ga komai a waje ba.cikingidan natsallake shafi Guda, gashi kamar haka..Sanyi da k'amshi ne zai fara dukan fuskarka saiwalkiyar tiles da fitulu su fara walle maka idosannan ka fara cin karo da kyatattun kujeru a wanikatafaren falo ga wajen cin abinci mai dauke dakujeru da tebur a tsakiyarsu, gefe guda kuma wani falo zaka taka wata matattakaka tayi kasa shima agefe.Ga makeken kicin nan mai d'auke da manya-manyan furuj da furiza da cooker gas, da kayankicin gaba d'ara koren launi ne aka had'a.Hatta cokulan dake kicin d'in koraye ne har lokokin kicin din. Dukuna uku ne a gidan, d'aya a k'asa kowanne daband'akinsa a ciki da gado d'an kamfani da madubida waduruf.Biyu kuma a sama makad'a- makad'an had'd'd'ungadaje ne ya fi na kasa, suma da bad'akansu a cikida wani katafaren falo a saman. Duk kusuwar gidan an ajiye fulawuyi irin na robarnan masu kama dana gaske.Ga kayan kallo nan dana jin kid'a a falukan.....kowanne d'aki kuma akwai talabijin an had'a ta datauraron d'an adam (settelite).Tunda Hanna ta shiga gidan kukan dad'i take a zuciyarta kuma tana hamdala tana yiwa Allah kiraritana gode masa.Allahu akbar.K'arfe 8 dai- dai bayan duk sunyi salloli sai Hasamyayiwa Hanna waya ya ce ta shirya ita dak'awayenta kawai banda tsofaffi da yara zai turo motoci azo a d'auke su matar gwamna ta shiryamusu liyafa a Tahir quest place har mutane sun farazuwa tayi sauri.Hanna ta shaidawa k'awayenta nan fa duk sukafara shiri.Ita kuma ta fad'a wanka ta fito ta tarar Haisam ya aiko da mota da wasu kaya da takalmi da jakarsuda ribon duk kalarsu d'aya ya ce inji matar gwamnata ce ta saka.Kayan kansu abun kallo ne wata shadda-shadda,leshi-leshi mai surfani riga da zani aniywa zaninkwalliya d'ankwalin kayan kuma an nad'oshi kamar goggoro irin kayan nan ne da ake d'inkowadaga Senegal to wannan na musamman ne sai irinmatan gwamnonin ne suke iya siyansu.Hanna ta saka kayan nan ta tufeke gashinta daribon kalar kayan ta d'ora goggoron kayan bayanhoda da jagira da janbaki da tasha tazo ta saka tsadaddun sarka da d'ankunne irin kalar kayan, gatakalmi da jaka ta d'ana.Sai kowa ya bude baki yana kallon kyau dagaAllah.Hanna ta zama kamar wata tauraruwa mai haske acikin taurarin masu disheshshen haske. Sai walkiya take,Hajir ta fesheta da turaruuka designers saik'awayenta suka take mata baya suka fito sukashiga motocin suka nufi Tahir quest place dakeLamido cresent...A bakin get din hotel suka iske Haisam da tulinabokansa suna zazzaune akan motocinsu sunajiran isowar su Hanna.Hanna na iso suka bud'e baki suna kallon ikonAllah. Ko a mafarki basu d'auka zasu ga amarya Haisamkyakykyawa kamar balarabiya ba.Musamman da suka je d'auren auren suka gawannan 'kauyen sai duk suka raina bikin sukacewa banda soyayya ma ne Haisam zaiyi da matark'auyen nan a bayan idonsa amma fa. Ashe wannan 'yar k'auyen ta linka matansu nabirni had'uwa.Suna ganin Hanna kamar idan kayi mata hausabazata iya mayarwa ba tsabar babu wata surartaguda d'aya data yi kama da bahaushiya.Ta k'aso ita da k'awayenta wajen da su Haisam suke tayi 'yar siririyar dariya ta duka kadan tagaishesu duk suka amsa.Haisam kam ko amsarwama ya kasa yi saimurmushi yake ya k'ura mata ido.Ya mik'a mata hannu wai su gaisa sai Hanna tasaHannu ta rufe ido. Abokansa suka hau cewa ai yanzu Hanna amaryakomai yazo karshe babu kunya Haisam ya zamamijinki.Haisam ya diro daga kan mota ya rike hannunHanna abokansa da k'wayenta suka take musubaya suka dunguma zuwa wani katafaren d'akin taro (conference hall) inda ake gudanar da liyafar,ashe jama'a jingim sun taru isowar ango da amaryakawai ake jira. Hall d'in haske ne tar kamar safiya ga wani sanyinna'urar sanyaya d'aki wasu dogayen teburan netafka- tafka a jejjer a cikin d'akin taron jama'a mazada mata zazzaune.Kwalayen lemune da kofuna tangaran da robarruwa a gabansu, gefe guda kuma masu kid'a ne da gangunansu a gefe 'yan police banda suna d'ankadawa a hankali kafin a fara gudanar da biki,Hanna na shiga taga idanuwa cununu akanta gabad'aya an tsaya ana kallonsu.Tebur guda Ramlah ce da k'awayenta had'ad'd'un'yan boko duk sun zubo mata ido.Hanna ta d'ago ta kalli Ramlah sai taga Ramlah tayi mata murmushi itama ta mayar mata.Koda kuwa ta had'a ido da sauran k'awayenRamlah sai harararta suke da kallon banza.Hanna ta sunkuyar da kai k'asa suka wucehannunta gam a hannun Haisam suka nufi kanwani k'ayataccen dogon teburi akan wata matattakala (high table) da k'ayatattun kujeruguda 2 irin na ango da amarya.Anan suka zauna sannan kowa ya d'au tafi.Abokan ango da k'awayen amarya suma sukasamu kujeru suka zazzauna.Baban abokin Haisam wani mai surutu mai suna Jibril (Jibson) shine take jawabi a lasifika.Bayan ya bud'e taro da addu'a ya ce ga matar maigirma gwamna nan da tawagarta suna shigowawace ta had'a wannan taron itama tazo taya angoda amarya murna.Kowa ya zauna yayi tsit ana kallon k'ofar shigowa wad'anda basu ta6a ganinta a fili ba suna so sugayaya take a fili wad'anda daman sun ta6a ganintasuna so suga wanne irin kayane a jikintamusamman mata masu tsegumi ana jira aga wanneirin leshi yau zata saka, wacce irin jaka kuma zatarike. Dan daman an san uwargidan maigirma gwamnaakwai iya tsala kwalliya kuma irin ta had'd'u 'yanboko, ga gayu ga kyau.Mai girma uwar gidan gwamna ce ta sako k'afartacikin katafaren dakin taron gefenta matarmataimakin gwamna ce d'aya gefenta kuma wasu daga cikin kwamishinonin gwamna suma sundoshi goma bayansu kuma wasu mata ne guda 2inyamurai suna sanye da riga sut da d'an gajerensiket iyakar gwiywowinsu sune body guards d'inta(S.S).Dogon tebur guda aka ware mata datawagarta.Suka zazzauna itace a tsakiya. Kayan jikinta irin nahanne ne shima ready made ne komai sak danahanna saikalarce ta bambanta, na hanna green nena matar gwanma kuma komai nata pink ne.Hanna ta kalli matar mai girma gwamna ta juyo ta kalli hanna suka hada ido tayi mata murmushi.Hanna ta juya takalli haisam taga shima murmushi.Tace yaya amma matar gwamnan nan tayi kama dawata kwata. Haisam yace kawarki. Nusaiba ko?Tace ashe kaima ka gani wlh sak nusaiba idris. Yayimurmushiyace ai ba kama bace nusaiba ce cewa tayi kar in gaya miki saidai kawai ki ganta. Hanna tadafe krji don mkk tana cewa wayyo Allah yanzuwnn nusaiba idris ce ashe zan sake ganin nusaiba aryw ta?Hall ya cika ya tumbatsa da hamshakan matanmasu kudi a hnkl hanna ta dinga hango wasu dagacikin kawayensu 'yan mkrtr su ta hango rauda maa zaune a gefen nusaiba. Tace ashe ruda zata girmatayi tsawo da kib? Bodane yake cashewa kannenramlah da haisam ne suke cashewa su amratu. Sai jibril mai jawabi a lasifika yace a bawa amarya daango fili su fito su cashe. Kowacce ta komata zauna.Hanna ta kalli haisam shin yana kallonta taji waninauyi yaya za'ayi tafito fili ta yi rawa ita da yayahaisam a matsayintana malaminta wanda takemutukar jin kunyar. Sai taji ya kamo hannunta suka mike gaba daya suka fara saukowadaga kan stage.Ramlah ta aikawanikaninta wajen masu kida tacepolice band ne zasu kdawa ango da marya wakarsarmadan kauna in tayi dadewa mutuwa ce kerabawa. Haka kuwa akayi police banda suka sakikida da waka. Ango da amarya ne kadai a tsakiyar fili. Ango ya tsaya cak yana kallon amarya. Itamamaryar a tsaye. Take ta daga kai tana kallonhaisam. Sai hawayeyake zubow daga idanuwanta,yasa hannuyana goge mata. Sai shimahawayen yafara. Diso masa, sai ramlah ta tasotazo tana ta zubamusu kudi abunka damata sarakan bidi'a nan fa kowacce tanaji da kudi ta budebakinjaka tanufo filidon ta yiwa ango da amarya liki. Jidda (hidaya) akaki kiranta dashi matar yaya habib. Ta karakarasowa filin ta Dinga yiwa ramlah liki da 'yandubu dubu ita kuma ramlah tana likawa mijinta daamaryarsa kudi. Matar gwamna haj. Nusaiba ta dinga liki ai kuwa police band da suka ga ruwankudi sai suka saka himma suna sakedukanganga.lall ai bikiyayi biki hanna ta rungumenusaiba da rauda sai hawayen farinciki sukeyi. Ba'atashi daga taro basai karfe 1:30 na dare. Bayanancinshaan cashe.Kwanan dangin hanna 2 a gidan amarya kawisuna shakatawa sai da kawu ahmad ya aiko yacemaza maza su hado su dawo sudukansukar a ragekowa snn sukatarkato suka tafiba'a son ransu ba.Hanna kuka suma kuka suka shigamotocisuka tafi.A hanyane dangin hanna sukayiwa iya haulehabaici ganin duk jikinta yayi sanyi ganinAllah ya sakawahanna da gidan tangaranma banasiminti ba. Wata kakar hannace ta fara cewa allahya bwa hanna gida, gida kamar ba'a duniyaba.Wata ta sake cewa oh har daake tadajijiyar wuyawaibaza a kai hanna gidan sumuntiba ashe gidan tangaran ma Allah zai bata, sauran suka tsomabakisuna yabawa inna haule mgn.inna haule tayi tsurutsuru a zaune a mota tasan daita ake tasantayikuma ba sharri kayi mata ba. Zaharaddeen Shomar Whatsapp 08168575100 GANGARJIKINSA NA AURA 3 Part 2 Posted by ANaM Dorayi on 05:39 PM, 30-Apr-15 Under: Gangarjikinsa ta Aura Bayan tafiyarsu masu iki matasuka shigo bagarenhanna suk hau kalkelewa suka wanke bandakunasukashishshinfida sababbinzannuwan gado sukafashe gidan da turarrukan kanshi. Wani kuku ne akicin yna ta shirya mataabincin kala kala.hanna tayikuri a zaune. Katafaren dakintdake sama itakadai sai talabijinta rasa meke damunta murna takekobakin ciki. Taji ana kiran sallar magriba sai tatashi ta shiga bndaki ta dauro alwalla tazo tashinfida abin sallatayi sallar mgriba da nafilfilo dtasaba. Ta zauna tana lazumi har sai da taji ana kiransallar isha'I snn ta tashi ta kawo sallarisha'I. Ta idartana linke abin sallar ne tji wayar dake ajiye agefen gadonta tana kara ta dauka a hnkl gamidacewa hello sai taji muryar wani bagwareneturanci yake yi yce madm nine kukun ki dagakicinmake yi miki waya na gama abinci ne jera mikiakn dinning table zn iya tfybabu wani abu da za'a dafa miki? Hanna taji wani abu banbarakwai waninamiji d suna hajara, Abu na frko daya bata mmkwi yu itace madam ke shida mata ngama abinci tazotaci kawi inhrma akwai wani bunda takeso adafamata ta fada, mmk na 2 kuma shine yaya za'ayi abar garjejen namijibama ba haushe bane ya shiga gidan matar aure yana dafa mata abinci daga ita saishi wnnba tsarinmusuluncibane. Hanne yace zi iya.Tfy banu wani bu da zaiyi mata. Tajimotsinbudekofarsa ya fita. Ta zauna a gefen gadotayishiru tana tnn.can ta tun she fa yanzu itamaryace,kuma tund babu kowa wata kila haisam ya shigo bari taje ta yi wanka ta sake tsala kwalliyairinta matan dasuka san darajr mazansu. Tayi sauri tafada bandaki ta dinga salla wanka ga sabulai nankala kalahar dana ruwa. Tana fitowa ta zauna kanmudubin dake shake da kayan shafe shafe ta fararangda kwlliya dafesa turarurruka suk jikinta. Tasha hoda da janbaki da gazalta zubo gashinkanta har baya bata tsrke ba ta barshi bazai. Tasaka wanidogon siket na jeans da wata yaryaloluwar riga bulawusmi dogon hannu dabuddden kirjin. Tsa wani takalmi mara nauyi maikama da sosan katifa ta fara saukowa daga kan bene. Tana isowa babban falon dake kasa saitajiwayar dake ajiye a falon tana kra. Hnna ta karsa knteburin dawayar take. A jiye tasa hannu ta daukasai tji muryar ramlah ce take fara'a tace helloamarya yaya kadaici ke kadai yau kowaya watseanbarki ko? Aiya don't worry haka rywr aure take sai a hnkl zaki saba. Amma yau bazan barki kikwana kadai ba zan kawo mikimai raya ki kwanagamu nan zuwa. Hanna tayi murmushi tace antyramla ina yini ramlah tace lfy lau kanwata gamunan ma zuwa saimu gaisa sosai. Suka ajiye kanwaya. Hanna tyi jigum a tsaye tana mmkn yadda ramlah take fara'a da nuna mata so da kauna tace aranta Allahkenan, ya hadani da duk abind zanjisanyi a ryw ta. To wa anty ramlah zata kawomin tatayani kwanina jin amratu ce kai ko dai haisam ne?Hanna ta dubi matsatstsun kayan dake jikinta tagagsky baza ta iya sakewa ba a gaban hisamba. Sai ta koma sama ta doro doguwar riga baka mai dankwali kafin t sauka sai taji muryarramlah tanasallama a fallon kasa. Hanna ta sauka tanarangwada ta karaso wajen da ramlah dahaisamsuke tsaye tayi dariya tace sannun ku da zuwakuzokuzauna suka zazzauna dukkan su fuskarsu cike da fara'a. Hanna ma ta zauna a kunyace tagaishesu, suka amsa ramlah tace munzomuciabincin don yau a nan zamu ci abinci intaya ku hirain tafi in barku, ko bakiyi abincin damu bane? Sai alkcn hannata dubi dinning table taga katan teburincike yake da manyan foodflask din abincitayimurmushi tace antyna isa in ki yin abincidaku, da ku akayi. Suka mimmike sukanufi dinningare. Haisam ne a tsakiya ramlah a gefensa na hagu,hanna na daya gefen, suka fara zuzzubawa a filetsuna ci suna hira. Ba sosai hanna dahaisam sukacika mgnb, ramlag ce take t zuba surutusun jinta suna satar kallanjunansu. Bayan sunkammala sukadawo kan kujerun falo suka zazzauna suna kallonwani film da akeyina gefensa rmla na daya gefennasa duk a doguwar kujerar suke.Haisam ya nisa yayi gyaran murya yace uwargida ramla tare da amarya hanna babu abindazance dku sai gdy ina fatan alheri a rywr mu gda 1ina fatn Allah ya bamu zman lfy. Ramla kece babba.Kuma Alhmdl kin nun halin manyakinyimanahalaccibabu abunda zance mikisai Allah ya saka miki da gidan aljannah. Ramlakin kasance mai tsananinhnkldatnn donhaka don allah inarokarki dakicigaba da yaddda kika fara kicigaba danunawakanwarki kuma abokiyar zaman ki hannakaunar da kike nunamata kadakisaurari mazugamasu zuwasuyi zuga don suhargitsama'aurata. Ramlah tayimurmushi tacehabahaisamy akamataka fahimce ni idan nasa raina ncezanyi bu gskybabu mai zugani in fasa. Ina sonka dayawa nagadace inso dukabindakakeso dan haka najihar rainainason hanna musamman na lura hanna nadaladabi dason zman lfy. I S Azamu zunalfy. Haisan yajuya ya klli hanna wacce kanta yake a sunkuyeakasa tanawsa dadan yatsanta yyi murmushi yaceamarya ke baki ce komai ba? Hanna ta dagokai tayimurmushi tace I S A zamu zaunalfy zan zama maibiyayya a gareku kuma ni tsakninadaku sai gdyAllah ya saka da alheri.Ramlah da haisam suka ce amin. Ramlah tayunkura ta mike tsaye fuskarta cike da fara'a takalli haisam ta juya ta kalli hanna tace to amaryyada ango zan tafi in barku sai da safe. Haisam yaceuwar gida tfy zakiyi bari mu rakaki har gidanki ko?Hanna ta mike suka dunguma suka fita suka nufi bangaren ramlah. Haisam na tsakiya suna tafe sunahira har kofar shiga bangarenta suka raka ramlah.Ramlah tayi murmushi tace torakyar ta isa haka kukoma ni dai gidunmawa tada zan baku anan itacena bawa kanwata kwana 10 da angonta ku hutasosai. Hanna tayi. Murmushi ta sunkuyar da kai tace a'a anty ramlah kwana ma 2 ya isa. Haisam yaharari hannayace maimakonkiyigdyshinekikekihar guduna kike? Su duka sukatuntsire da dariya. Ramlah ta juya ta shiga gida taceni dai na barku lfy sai da safenku. Tanashig ta turokofa ta rufe tasa mukulli ta bame sai ta sulale ta zube a kasa yayin dawani zazzafan hawaye yadinga zubo mata tsananin kishiyakamata sbd tanason haisam matukar so babu yadda taiya dole tasoabunda yakeso.kishikumallon mata.Haism da hanna sukajuya sukanufi bangarenHanna, suna tfy a hnkl suna hira. Hisam yakai hannuzai rike mata hannu sai yaga ta goce tayi gefe.Haisam yayi murmushi yce Allah ya bakihkrhannata na fasa rike mikihnnun tunda rowa akeyimin. Suka shigo cikin gida haisam yajawokofarfalon ya datse. Haisam yace da hannazo muje sama muyi sallah. Hanna talangwabe kaicikin siriyar murya taceyaya nayi sallar isha'I tundazu. Haism yayi murmushiyace ai nafila zmuyi. Tamike kanta a sunkunye akasata wuce gab hasm nabiye da ita suka hau sama. Daki hnna ta wuce kai tsaye ta shiga bandaki, haisam kuma sai ya shigadaya dakin yana shiga sai ya cire kaynsa ya duratawul ya shga bandaki don ya ske wats ruw.Jikinsa byn yayi wnkn ne ya dauro alwalla yanafitowa yawucewajenkatuwrwadruf dake dakinyabude wani bangare kyn sawarsa ne da kayan bacci. Ya zbi wasu kayn bacci masu kyau da laushitubus auduga ne zalla rig ce gjera iy cinyami dogonhnnud dogon wando farare ne sol anyi musufulawa da kalar shudi sababbine gar a ledarsu yaciroya saka a jikins ya juya ya nufi wajen madubiwanda aka dankareshi d mayukan shafawa masukamshi da turrarruka designers. Ya shafejikinsa da mayukan nan masu kamshi kana yafeshe duk ilahirin jikins datufafns datsdaddunturarurruk masu masifar kamshi wnn na cewawane wnn sukahadu sukabda wani daddadunkmshi. Haisam ya dauko comb y taje gshinsa ya mulke da man gashi mai kamshi , hakika ko shi dakansa yasan yayikyaua daren nan blle wacce yayidominta. Ya fitoya nufidakin dahanna take zauneyashigo my love na barki kina jirana ko? Tayimurmushi tace ba komai ai.Baka dade ba, ya budewadruf ya dauko watakatowar sallaya ya shimfidaya juya ya kalli hannato bismillah zo ba yana ki tsaya zamuyi sallah raka'a2 ta gdy ga Allah dayanunamana wnn ranardamuka zama miji da mata da kuma yin add'uaAllah ya kade man duk wata fitina ya bamuzmnlfy da zuri'a ta gari koba haka bane? Hanna tasahnnuta rufe idosbd murna da farin ciki daya rufeta dakunya tace haka ne yaya. Ta tasotazo ta tsaya abaynsa suka tada kabbarar harama. Bayan sun idarhaisam ya daga hannu sama yana kwararo addu'oihanna na amsa masa da amin daga karshe suka shafa. Haisam ya juyo yana kallon hanna kallo maikunshe da tsananin soyayya da sha'awa jiyketamkarya hadeyeta a daren yau. Ta sunkuyar dakanta kasa tana murmushi maihade da kunya.yanisa yace zonan kusa dani hanna. Ta matso kusadashita zauna yace nan kusa dani zaki matso sosi. Ta sake matsowadaf dashi ta zauna yasa hannu yashafa gefen fuskrtaa hnklhar zauwa gefenwuyantayayinda dankwalin ta ya sulale zai fadi kasatayisauritaja dankwalinta daura ta danja da baya.Yayi murmushi yace ja da baya ma kike? Naga doleki cire wnn bakar doguwar rigar da dnkwalin ki saka rigar bacciko dasu zaki kwana? Hannatagyada kai tace dasu zan kwana. Haisanyayi dry ya mike yje ya bude wadruf ya zabowahanna wata tsaleliyar rigr bacci. Rigar yar karamaceiya gwiwa yaloluwa marar nauyi mai shara shara.Kalar pink ce anyi mata kwalliy da wani gshimi lushi a ksn rigr dwuya,hnnun rigar dn siriri ne wandaza'a iy daure shi ko a kwance. Ya cirota daga ledaya mikewa hanna yace in ganin gr kis wnn zakifijindadin bacci tunda bata da nauyi . Hanna ta karbata daga rigar don taga yaya girman rigar take, saitajigbnta ya fdi sbdit a gsky tana jin nuyi d kunyar yaya haisam yaya z'yi taiya sa wnn 'yar rigar agabansa. Tana son haisam matukar amma bata jinzta iya kwana a gado 1 dshi zucyrta na tuna matayadda haisam yake da girma da kima a idanuwantatamkar wani kawunta take gninsa sbd dawiniyar dyashada ita tun tana yrny.hisam tace tshi ki saka k inzo in taya ki balle mabllin. Hanna tace a'a ta miketatafi can lungun gado ta cire dnkwalin rigar ta ciredoguwar rigr sai mtsatstsen siket da rigr da sukajikinta (body hook) haisam ya koma kujera da takegaban mudubi ya zauna yayin da idanuwansa suketsaye cak a kan hanna, ta juyota dubeshi taga ita yake kallo sai ta dauki rigar baccin ta nufi bandaki.Haisam yace ina zki kuma? Cikin kunya kanta akasa tace bndaki zanje in canja. Hism yabude bakizaiyi mgn sai wayarsa ta fara kara. Hanna ta fadbndaki ta rufe kofa tasa mukulli ta bme, ya dubayaga maiyi masa waya sai yaga safiynu ne abokinsa daga kd, ya dnna yace safiyanu yyakake?v safiynu ya kyalkyale da dariya yace damannabugone don inyi tsokana in dama ango da amarya,haisam yayi driyayace bbu kyau fa zk duki alhaki.Sfiyanu yce tunda baka yi brci ba yanzu taimaka kadubomin lambr shafi'u na dubai ke cen saika zuna, yihkr ka bani ynzu sbd gobef zn tafi dubai inaso inneme shi idn naje can. Haisam yayi jiyar zuciya yacesafiyanu banda kai wlh da bazn fita ba a yanzu sainaje mota fa snn zn dubo mka diary na. Safiyanuyace nasani abokin taimaka min nsan abun is noteasy ngo dnye shrab kamr ka, ka fita kabar amarya at this lte hours sorry dan allah, ka mika mingaisuwata zuwa ga knwata hanna. Suna hira awaya haisam ya bude kogar dakin ya fita ya saukokas ya bude ya nufi wajen da motoci suke.Bayan hanna ta shiga bandaki sai ta fad wankata fito,ta saka rigar ta dubi kanta Madubi tagantatamkar wata baturya rigar tayi matukr yi mata kyauhar da wani ribon na daure gashi a sakale a jikinrigar. Hanna t dure gashinta dshi. Sake kallon kntaa jikin madubi sai taga duk ilahirin jikinta tan gani a cikin rigr sita girgiz ki tace Ranta gsky baxn yardayaya haisam ya ganni a haka ba, ta tsaya tyi shiru abandaki tana tnn ydd za'ayi ta fito a haka. Ta budewta lokar glass dake makale a jikin banfo bandakinsai taga abubuwa ne kala kala na gyaran baki ,masu sa baki yayi kamshi, huci yayi wasai. Ta fra karnta jikinsu 1 bayan 1 don tsan amfnin su yaddaza'ayi amfni dsu. Bayn tayi brush sai ta shigadaukar kownnensu tana amfni dashi. Na kuskurebkitakurba ta kurkure n feswa ta fesa. Sai da tadauki tsawon minti 15 tana abu 1. Data gama istazo ta bude kofr a hnkl ta leko is taga haisam bayanan, ta fito daga bandakn ta ske duba ko inahaism baya nan taji dan snyi a ranta don da fargbada kunya sun isheta. Ta nufi gban madubi nan fa tazauna tana ta rangwada kwalliya shafe shafe dafeshe feshe turare. Hnn ta klli kanta da kanta tsndole ne ma yu haisam ya rikice sbd tayi kyau sosai. Bayan ta gama kwalliy ne ta tashi daga gbanmadubin ta tsaya cak a tsakiyar dkin tana shawararkofa da mukulli tyi kwnciyrta ne, ko kuma ta komabandaki ta rufe kanta ne? A gsky yaya haisam bazaiji dadi ba ita kuw batason ta bata mas rai kokadan a rywr ta sbd haism bi taba bari wani ya bata mata rai ba balle shi da kansa burinsa kullum yafaranta mata ya ganta cikin farin ciki.Bayan ta gama kwalliy ne ta tashi daga gbanmadubin ta tsaya cak a tsakiyar dkin tana shawararkofa da mukulli tyi kwnciyrta ne, ko kuma ta komabandaki ta rufe kanta ne? A gsky yaya haisam bazaiji dadi ba ita kuw batason ta bata mas rai kokadan a rywr ta sbd haism bi taba bari wani ya bata mata rai ba balle shi da kansa burinsa kullum yafaranta mata ya ganta cikin farin ciki. Ji tayi burumya bude kof y shigo, ta tsorata taja da baya. Hisamya kura mata ido yana yi mata murmushi ya turakofar dakin ya rufe da mukulli ya nufo inda hannake tsaye a hnkl. Yasa hannu 2 ya jawota kan kirjinsa yarungume ta tsm yayin dadukkansuzuciyoyinsu suka hau bugawa a lkc 1 kownnensuyana jin yadda ta dan uwansa take bugawa dontsananin farin cikin da suka tsinci kansu a wnn lkc.Kowannensu kwakwalwarsa na kokarin tatantance masa shin dagaske ne ko kuwa mafarki sukeyi. Hanna ta dago da knta hnkl ta kalli hisamdon ta tabbatr shi din ne kuwan daidai lkcn shimaya dago yana kallonta don shima ya tantance tnnda yake irin nahanna ne. Cikin sanyayyar muryahaisam yace hanna kece kuwa ko mafarkin kinakeyi kamar yadda na sabayi kullum? Dakyar ta iya mgn ta gyada kai ta kashe ido yace abundanakeso in tabbatar kenan don nima ina kokonto azuciyata. Kafin ta rufe bakinta sai taji bakinsa cikinbakinta. Nan da nan ta sulale ta tsugunna agananta yasa hannu ya dago da fuskartayayi matakallon ido cikin ido yace kada ki manta ada GANGAR JIKINKi bata tare dani RUHINKI ne yke taredani, amma a yanzu GANGAR JIKINKI DA RUHINKIsuna tare dani don haka karki ji nauyi na ni mijinkine. Ya mike tsaye ya jawo hannuntaya tashetatsaye suka zubawa juna ido. Ta kashe idocikinzazzakar murya tace jaine farincikina abun yardata, abunda nafiso a rywr tana mallaka maka GANGARJIKINA. Ta dora kanta akan kirjinsa ta lumshe idoyayin dashi kuma yasa hannunsa 1 ya rungume tayasa 1 hannun yana shafar lallausan gashin knta.Hakika ma'auratan nan yau sunfi kowa farin cikiarywr su jinsu suke tamkarba'a cikin dny suke ba domin a wnn dnyr tamu akwai bacin rai su kuwabasaji, ana ciwosu kuwa sumul suke jisai tsantsarfarinciki da yake nukurkusarsu. A tsakuyar gadojhannata jita yayin dahaisam ya shigasumbatarta,yana shinshinata, yana lasar dukilahirin sassanjiknta. Sai a yau hanna tasan tayi aure kuma ta sami tsantar soyayya da yadda akeyinta, ashe bello mdushafar mai yake yi mata baisan yaya akeyinsoyayya ba. Kuma shima hasam sai a yau yasanyayi aure don a zuciyarsa a dagule take hnkl sa atasheyakeidan yana tare da ramlah sjikansa bai sansanda yake yiwa hanna wasu abubuwan ba sun raya daren yau da sunna.Yau ango da amaryarsa idanunsu basu ga barci ba.A kunnensu aka kira assalatu.Dakyar da sud'in goshi Hanna ta samu ta zarejikinta daga jikin Haisam don ya cukuikuyeta yarungumeta k'am kamar zai fasa k'irjinsa ya zurata a ciki.Hanna ta mik'e da kyar saboda duk ga6o6inta sunjigata, ta shiga tana shiga ta sakarwa kanta shayarruwan zafi ta dai-daita ta surka da ruwan sanyi dai-dai wanka.Bayan ta gama wanka sai ta d'auro alwalla ta fito sai Haisam ma ya shiga.Bayan ta fito ne sai yasaka wato doguwar rigaHanna kuma ta saka bak'ar doguwar riga maid'ankwali suka yi jam'i suka yi sallah. Basu bar kansallaya ba sai da gari yayi haske kamar k'arfe 7 nasafe suna lazimi da hailala da hamdala ga ubangijinsu sarkin sarakuna daya basu dama ikonyin aure sbd suna tsananin k'aunar junansu.Hanna ta mik'e tabar Haisam a zaune yana jan carbita fita ta sauka k'asa ta shiga kicin.Butar ruwan zafi ta jona ta cika flask saita fasa kwaida yawa ta soya waina masu kaurin gaske ta zuba a faranti ta d'ebo ta hau sama.A kwance akan gado taga Haisam har ya fara d'anbacci, bud'e kofar da tayi ne ta tashe shi.Ya d'ago ido ya dubeta sai yayi murmushi ya ce"Daman kicin kika shiga da sassafen nan?"Hanna tayi dariya tazo ta ajiye k'atan faranti me dauke da plate din wainar kwai da flsk din ruwanzafi.Ta sake fita falo ta d'auko wani faranti mai d'aukeda kofuna 2 da cukula kanana da madara, sukarida milo tazo ta ajiye a kusa da da farantin farko, tak'asaro wajen gado inda Haisam yake kwance ta durk'usa har k'asa cikin sassanyar murya ta gaisheshi, ya mak'ale murya yana kwaikwayonmaganarta ya amsa.Su duka suka tuntsire da dry, Haisam ya tashi zauneya zuro k'afafuwansa k'asa daga kn gado ya jawoHanna jikinsa ya ce "Hanna ai yanzu nafi k'arfin gaisuwar ina kwana yaya a wajenki.Kinsan irin gaisuwar da zaaki dinga yimin?"Hanna ta girgiza kai ta ce "Ban sani ba."Ya ce "Duk sanda zaki gaishe ni idan ni da ke saikizo ki tsotsi bakina ki rad'a mun a kunnegaisuwar, idan kuma da mutane a wajen saiki mik'a min hannu mu gaisa.Irin wannan gaisuwar zaki dinga yiwa yayarkiRamlah ki mik'a mata hanna kuyi musabaha sannaku gaisa.Hanna tace zanyi yadda kace insha Allah. Yayimurmushi yace na gode mu lobe, af na manta bantambayeki ba yaya jiya? hanna ta rufe fuska datafukan hnnunta tace shiysa naga ya dace kashadan ruwan tea da sassafen nan sbd naga ka gaji.Haisam ya harareta yace au nine mana gaji banda ke? To gobe ko ruwan tea din ma baza ki iya tashikidora bani da ke zanga wandazi iya motsi da safeai tausayinki naji yau. Hanna tayi dry tace yi hkr danAllahni ba haka nakenufi ba. Bayan sun gama karin kumallo ne suka koma kangado suka kwnta. Hanna na kwance a kan kirjinhaism tna shafawa a hnkl yayin da shi kuma yakeshafar gshinta da gefen fuskrta ya zauwa wuyantasuna hira mai dadi har barci mai dadi ya sure su,kowannensu ya dora da mafrkin dan uwnsa.basu tashi farkawa ba sai krfe 2 saura kwat ana sallarazahar. Bayan sunyi wanka sun caba ado sunyisalla sai haisam ya kama hannun amaryarssukanufi bngaren rmlah wcce tuntuni tasa anshirya musu abinci kala2 da yake tsan anan zasudinga cin abincin rana dana dare sbd haisam ya dakatar da kukun hanna sai nan da sati 2 snn zasuzo suci gba da yin abinci kada suzo su dame su, surage musu wani bangare najin dadi. Ramlah na ganinsu ta taso da fara'a da murna tazota rungume hanna snn ta rungume haisam tasumbaci kumatunsa tace kun tashi lfy? Suka amsamata da lfy lau. Ta kaisu wajen katafaren teburn cinabinci mai dauke da nau'ikan girke2 kala2. Sunacin abinci suna hira suna tuntsira dry kai kace gidan biki ne. Haisam ya iya surutu da hirahakaRamlah ma tana da mgn hanna ce dai sai tayi ddagaske tunda ita ba gwnar surutu bace. Tana jinsusuna ta surutu saidai tayi dry idan na dry ne idankuma haisam yayi mata tsiya sai ramlah ta shigarmata. Tana tare mata don ita bata iya surutu ba sosai kuma ko ba hakaba tana ganin haisam daramlah da wata kima da girma a wajenta don hakatakejin nauyin tayi ta shiga hirarsu da zolaye2 dasuke yi. Da suka gama cin abincin sai suka koma knkujeran falo suna kallo. Haisam da ramlah akandoguwar kujera suke zaune, hanna kumana wata kujera a gefensu.suna kallon kaset din bikin hannada haisam na shagalin da akayi a tahir guest palacewanda dan asharalle,boda da police band sukacashe. Ango da amarya aka dallaro a tsakiyar filiyayin da suk kurawa junansu ido hanna nahawaye a kaset din. Ramlah tayi jiyar zuciya tace soyayya. Haisam ya dan harareta yace meye wanisoyayya. Ramlahta tuntsure da dry tace meye toabun hararar don nace soyayya, kawai cewa nayisoyayya masoya na gani. Haisam yayi murmushiyace nasan da mgn a bakinki hana. Ramlah kece fa,nasan halinki sarai. Tayi dry tace da dai zance wani abu amma nafasa tunda har kasa a ranka zancewani abu. Haisam ya jawo hannunta. Ya murdeyace sai kin fada zan sake ki. Hanna tayi murmushitace yaya haisam karka karya mun anty na fa.Ramlah tayi dan kara tace yallabai yi hkr sakeni zanfada maka. Haisam ya sakar mata hannu yace to fadi ina sauraren ki.Ramlah ta gyara zama ta dubeshi tayimurmushi tace kafin in fadi abinda zan fada donAllah zanyi muku yan tambayoyi zaku amsa min?Haisam yace zamu amsa miki yaya zamuyi tundaAllah ya hadamu da 'yar jarida. Ta juya ta kallihanna tace kefa kanwata , idan na tambaye ki zaki bani amsa tsakani da Allah, akwi abunda nakesoinji ne sai in hada in fadi abunda yake raina. Hannatayi murmushi ta sunkunyarda kai kasa tace mai zaihana in baki amsa anty na zam amsa duk abinda nasani I S A. Ramlah ta jawo lokar jikin centre tble tadauko wani dan littafi da biro tace yallabi ta kanka zan fara tambayoyin. Ya gyara zma yace ina jinki,sharadi 1 idan kikayi min karkatacciyar tambayasaina kara murde miki hannu. Ramlah tayi dry tacena yarda. Tambaya ta farko itace zaka iya gyamunyaushe ka fara son hnna a zcyr ka. Hanna ta juyo takurawa haisam ido tanason taji amsar da zai bata. Haisan yayi shiru cn yayi murmushi ya dago ya kallihanna ya juya ya kalli ramlah yce tun ranar danafara ganin hanna naji ta kwant mun a raina amatsayin 'yar yrnyr daya kamata in taimaka wa ahnkl kuma sai naga tana da hali nagari kamarladabi da biyayya, kunya, tawakalli, hkr, sanin y kamata, tsafta, tausayi dadai sauransu sai naji tanasake shiga raina amma bazan ce a lkcn soyayyanakeyi mataba sbd yrny ce. A hnkl kuma sai najihanna ta hau wani matsayi a zcyr ta wnda ya wucena sabo ya zama idan tnn nake to tnn zanyi hakakuma idan ina hangoni da matata ta aure sai in hango hanna, daga nan kwakwalwata ta tantacemun son hanna nake saina danne shi a zcyta nakasa furtwa sbd wasu dalilai nawa masu karfi.Haisam da hanna suka hada ido sukayiwa junamurmushi. Rmlah tayi ajiyar zuciya tace nagode saitambya ta2 kakan tuna hanna a zcyr ka kamar sau nawa a rana? Haisam yace ko ina ganin hanna kobana tre da ita koda yushe ina tnn ta. Ramlah taceita kuma tsohuwar abokiyar zamanka meyematsayinta a zcyr ka tsakani da Allah. Su duka 3suka tuntsure da dry. Haisam yace ita anty ramlahda farko bana ra'ayin soyayya don ni har kunya nakeji idan aka ce ina da budurwa daga bay nagalallai2 anty ramlah na sona da gaske sai naga yakamata in aure ta. To akasin da aka samu har tabani haushi shine da naje na durkusa har kasa inarokarta tyi min izini in auri hanna taki. To shinenima na toshe mata hanyar walwala kamar yadda ta hanani nima. Su duka suka tuntsure da dry.Ramlah tce da fatan yanzu an bude mata hanyarwalwala tunda ta bude maka itama. Yayi dry yace aituntuni ma zancen da akeyi yi yanzu babu matsalaina sont sosai. Ramlah tayi jiyar zuciya tace Allahyasa haka ne amin. Ta fara rubuce2 a jikin takardai dake hannunta. Can ta dago ta dubi hanna tacekanwata gareki na dawo, shin yaushe kika fara jinson mijinki haisam? Haisam ya zura mata ido kemyana kallonta .Hanna ta gyara zama tayi murmushi tace yayahaisam dai wani muhimmin mutum ne a rywta.Tamkar dan jariri ne wanda ya budi ido damanwacce ya kamata ya far sani a dny ita cemahaifiyarsa. To haka na kasance ina bude donasanda na fara sanin meye ryw yaya haism na fra sani don haka shine wanda na saba dashi, danafara sanin meye so is tsuntsun son ya fada akansa,na kasance kod yaushe shine a raina. Murmushikwai haisam yakeyi rmlah tce hka ne nagodekanwata. Ta sakeyin rubuce2 daga karshe ta rufekittafin ta jiye a gefe ta dago ta dube su tace dlilin da ysa nayi wadannan tambayoyin shine akwaiwani shiri da nakeyi a zcy ta in har mijina ya baniizini inaso in fadakar da matsa samari da yanmatagame da soyayya sbd na koyi darussa da damaakan wnn lamarin naku. Haisam yace ki fdakar aina? Ramlah ta nisa tce a matsayina na wacce ta karanci harkar yada lbr ko ince 'yar jarida a gidanradio mana. Haisam ya girgiza kai yace bzan yardawani kato ya dinga jiye min wnn zazzakar muryartaki ba. Hanna tace ai bashi da aibo don mace tayiaiki a gidan rediyo. Ramlah tace yauwa kanwatafada masa, ni bama aiki nace zanyi ba kawai a sati sau 1 zanyi shirin kuma ni zan dauki nauyin shirin.Haisam yace meye shirin? Sai cewa kike shirrinfadaminme zaki ce acan kuma yaya sunan shirin?Ramlah tayi dry tace ni dai zan fadakar akan soyya.Macece soyayya, kuma yaya ake yinta, kuma dawayakamata ayi? Haisam yace haka sunan shirin kenan dawa ya kamata yi soyayya? Ramlah tace sainayi tnn dai insan sunan shirin da zansa. Kanwatako zaki. Zabar min sunan daya dace in sawa shirin.Ta tmby hanna . Hanna tayi dry tce anty kisawashirin suna SOYAYYA GASKIYA CE. Haisam da ramlahsukahadabaki suka ce soyayyagsky ce. Ramlahtace gsky sunan yayi, haka zansa masa kanwata kincewani abu kema ina fatan zaki tallafa min shirin yayifarin jini wajen bugomin waya da bada shawarwaria FREEDOM radio zanyi shirin insha Allahu in yallabaiya barni. Kaga itama kanwata hanna sai ta rubutajamb wnn shekarar ta karbo result dint tazo ta shig B U K ni kuma ina yan shirye2 na a gidan radio donni ina balain sha'war yin aiki a gidan radio kotelebijin tun ina yry don haka nema na karancimass com. Kefa hanna me kike sha'awar karanta.Hanna tayi murmushi tace nidake sciences nayi asecondary ina sha'awar in karanci medicine ko biochemistry. Haisam ya dube su dukansu ya turahula keya yace ku gama sha'awar ku ina jinki basai na barku ba. Ramlah tace haba yallabai ya zaka yi mana haka saikace wani mutumin can kauye, kamar wani tsohokake kokarin hana matanka kara2 da aikin da zaiamfani jama'a. Kaga yanzu kamata yayi karshenwatannan kai da amaryarka ku fita honey moonzuwa wasu kasashe kuyi kamar wata guda acan, ni kuma kafin ku dawo na fara shirina a FREEDOM.Haisam yace to uwar tsari tsara mana tfyr waccekasa da wacce zmuje. Ramlah tace kaga da farkoku fara zuwa dubai daga can sai london ku hutasosai, ku wuce america da germany daga can saiku wucce saudia kuyi aikin hajji tunda lkcn aikin hajjin ya kusa ina ganin daia wata 2 zakuje kuzagayo ku dawo. Haisam yadubi hanna yace hannahaka yayi miki.Hanna tayi murmushi tace yayimun tunda hakayayiwa anty na aini bani da zabi. Ramlah tace hakaza'ayi yallabai ni kumasai ka barni in fara shirina agdn radio duk sati. Haisam yayi dry yace naga kindamu da wnn shirin naki to na barki kije kiyi Allahya taimaka miki. Idan kinji an fara saida form din jamb sai ki sayawa hanna idan a lkcn bama nan.Kafin mu tafi zanje kazaure in karbo matasakamakon jarabawarta, is ki cike mata form dintazo ta zana jarabawrta sai ta shiga B U K shikenanku skar mun marata in hut zance ya wuce ko? Sukahada baki dukkansu sukace mungode. Murna ce ta lullubesu dukkansu musamaman hanna sai take tananata sunayen ksashen nan a zcyr ta Dubai.London, america makka. Lallai waya gahnna a turai,har aikin hajj zanyi, yadda hanna takeso tajemakka sai gashi ko sati batayi ba a gidan miji anbiya mata makka. Sai hamdala takeyiwa Allah a zuciyarta. La'asar tyi sai dukkannin suka tshi sukayialwalla suka yi jam'I sukayi sallr l'asar suk ci gba dahirr da kallon talabijin salla ce kawai take tshin su.Byn sunyi salla isha'I ne suka wuce teburin cinabinci suka ci abincin dare ramlah ta raka su harbangaren hanna tayi musu sai da safe ta dwo nat bngaren. Hanna tna mmkn irin wnn kirki irin nakishiyarta ramlah ashe yanxu akwai kishiyoyi irinramlah da zcy 1 take abinta wasa da dry. Hakikanayi dace da miji da kishiya ta gari. Hanna ta fada azcyr ta. Babu bacn rai a zcyr hanna a yanzu sai farinciki ko ina ta waiga. Haka Allah yake ikonsa ai, Allah mai girma. Kwanan haisam goma a dakin hanna kamar yaddaramlah ta amince masa yayi.haisam da maryarsahanna sun cancare da amarci. Cikin kwana 10nan.Sun farantawa juna an faiya ce irin son da sukeyiwajuna. Bayan sun idar da sllar isha.I suka wucew kanteburin cin abincin suka ci suka koshi kmar yadda sukeyi kullum a bangaren ramlah. Sai haism yacesu taso suje gidansu su gaishe da hjyr sa. Haisamne yake tukawa ramlahce. Ta zauna a gidan gabatunda itace zata karbi kwanan a daren yau.Hannata zauna a kujerr baya. Suna ta hira wasa dadry a hanya harsuka isa suleimn cresent ciki gidansu haisam. Hjyr haisam tayi matukr yin farinciki. Hnkl haisam akwaance itama sai farinciki yakamata. Hanna da ramlah suka durkusa gabadaynsu a gaban surukarsu suka gaisheta cikinladabi da biyayya. Ta amsa musu cikinfra'a gamidayimusu nasihohi akan suci gaba da zaman lfy kamr yadda suka fara kada su sauraru 'yan zuga.Su toshe kunnuwarsu sbd wasu mutane suna dabakin ciki bsa sosuga ana zaman lfy. Taci gaba dacewa zaman lfyr su shine farin cikin danta haisam,farin cikin haisam kuma shine kwanciyar hnkln tadaga karshe tayi musu gdy da fatan alheri. Lemuna da snacks kala2 tasa masu aiki suka kawo musu.Bayan sun sha hira sai haisam yace su taso su tafi.Har bakin kofa hjyr haisam ta rako su tayi musu saida safe snn ta koma gida suka. Shiga motasuka tafi.Gidan yaya hbib suka nufa da yake hotoro GRAsuka daki gurbi don yaya habib baya gida amma matarsa hidaya tana nan. Ta tare su da fara'a tarungume aminiyarta ramlah suka shiga cikin daki.Hanna da haisam suka zauna a falo suna kallontalabijin din dake kunnne. 'Yayan yaya habib guda2 zakar da nana sukazo wajen hanna da haisamsuna taya su hira. Ramlah da hidaya suna cikin daki a zazzaune a gefen gado, hidaya tace kinsanmeyasa na jawoki daki muka kebe? Toba wani abubane illa ince ni dasu aisha suke da hauwamamman muka fga mun dace muyi miki nasiha wlhramlah kin bamu mmk duk wnn zafin naki ashe nabanza ne ina bakin naki na masifa har kika yarda kika zama baiwa 'yar kallo sbd wata yrny 'yarkauye. Gata zata kwave miki miji. Ramlah tayi ajiyarzcy tace ai har meetn kuka shiga a kaina ke dasuhauwa mamman? Hidaya tace eh mana daman jibimukayi zamu hadu a gidan aisha sule muje gidankidan dole mu fada miki gsky akan bun da zai cuce ki meye kawancen idanbamugaya mikiba wa xai fadamiki. Wlh wnn 'yarbuzuwar da kike gani kina wanikara wayar mata da kai sai ta waye taci ta koshi saita mamaye gidan ki zama yar kallo. Ramlah tacehaba hidaya yanzu ke da kanki kike cemin haka?Bayan kinga duk tshn hnkln da haisam ya shiga da iyayensa da danginsa gaba 1 a sanadiyyar rabashida hanna. A gaban idona da bayan idona babusurutun da ba'a yimin ba na nacewa haisam nahanashi ya auri wacce yakeso gashi nan nima bansami soyayyarsa ba. Yanxu Allah ya amsa addu'ataya kuma yaye mun tsananin kishi ya cusamin kaunar hanna muna zaune kalau damijinakamekowacce mace yanxu hidaya ba is ku tayanida addu'a ba da fatan Alheri Allah ya kar munjuriya da cigaba da samun zamn lfy ni da abokanzamana ba. Ramlah na rufe baknta saisuka jimuryar haisam ya leko yana cewa to kus2 din ya isa haka ku fito a hadu ayihira har hanna. Hidayahaka ake karbar baki? hanna ce bakuwa sai kija'yar gida daki ki bar bakuwa a waje byn kawo tanayi itama ta saba da dangi. Hidaya da ramlahsukayo waje ramlah tayi dry tace kuyi hkr inakallon kyn jarirn data suyone kasan ta kusa haihuwa. Hidaya tatabe baki tace wa yaga bakuwaai ni nan daka gann bana marhaban da zuwanamarya koba tawa bace balle abunda yayi ramlahshi yayi ni. Haisam ya dan harareta yace banganeba?hidaya tace hak zaka ce mna wnn bkuwarda kake cewa nayi nace bana marhaban da zuwan ta sbd ni Allah bi samin son amare bame za'ayidsu,su shigagidasu tarar da maceda'ya'yanta suyikane2 su kwace mata miji idan ba'ayi sa'a bamasaisun fitar da ita. Ni ramlahna sani saikai duk watabakuwa ban santa ba. Ramlah tajiwani yarrajikintanuyi dakunya suka rufetatayi sauri ta katse hidaya tace hanna aikanwarmuce bari in daukomata lemo ma a kicin. Ta yunkura zata tashi haisamyasa hannu ya dakatar da ramlah yace ramlahbarshi ba komai, ba sai kin dauko mata lemo batunda matar gidanbata dauko mata ba kema bazaki daukoba tunda ma tace hanna ba bakuwarta bace ai is mu tashi mu. Tafi inda akenemanta akekuma sonta. Hanna ta sunkuyar dakai kasa jikintayayi sanyi kalau . Hidaya ta sake yatsine fuska tacelallai rmlah sannu da kokari irin wnn rawar kanmijinki yakeyi kan amaryrsa 'year gwal ce kenanba'a tabta. Hanna ta mike tayi wuf ta fice da sauri ta nufi wajen mota tatsaya yayin da gabanta yahaufduwatna fargabar kada fa hidaya ta zuga ramlahta canja musu ynayin zamansu in har ramlah tacanja hali lalli hanna zata shigahalin kunci muddinsuka shigayin tsiya2 da ramlah. Hawaye ya zubosharr daga idanuwan hanna ta jingina kanta a jikn mota tana hawaye. hisam ya tsaya kawai yanakallon hidya haushinta ya hanashi tunano kalmardazi fadamata ya girgiza kai ya juya ya dubi ramlhwacce itama tayi tagumi a zaune ranta ya gama bacisbd abundakawarta tayiwa kishiyarta.Yayi ajiyar zcy ya ce "Ramlah ai kinji abundaHajiyata ta fada muku d'azu ko dn haka ki kula, kikiyaye sai kin toshe kunnunwanki sbd 'yanzuga,'yan neman kar a zauna lfy kiyi amfani dahnkl da tunanin sai kinyi yak'i da zcyrk kinyi watsi d wasuwasun da ake cusa wa zcyrk na munananshawarwarin da ake ba. Gaskiya Hidaya ba Hannakika wulak'anta ba ni kika wulak'anta don Hannabata san hanyar d'akin ba ni na kawota kumaHanna bata auro kanta ba sai d na aurota nazo nahad'a t da Ramlah, bnji dad'in abunda kika yimin ba Hdy ko yayana Habib ne yayi wa Hanna irinwannan walakanci zan fada masa gaskiya kumabazan sake takowa gidansa ba har abada balleHanna tazo.To amma yanzu tunda ba shi bane yayi mun hakabazan ce na daina zuwa gidan ba kwata-kwata tunda donshi nake zuwa, ngd sai anjima." Ya mik'eya fita a fusace.Ramlah ta k'uga da k'arfin cikin fushi ta ce"Hidayaya zaki mun haka? Me yasa kika mun hakaHidaya?" Ya kike so nayi da rayuwata?" Hidya tata6e baki ta ce "Dalla banza kema 6acin rai kike don nayiwa kiyishiryarki wulak'anxi, ni Ramla kinabani mmk wlh duk yadda akayi wannan amayartaki ta shanyebki." Tasa hannu zata riko Ramlahdon taga Ramlah tayi matukar damuwa Ramlah takauce ta ce "Banji dadi ba gsky yau kin 6ata munrai." Ramlah ta miki ta fita.Hidaya ta bita da kallo hr ta fice.Tayi murmushi ta rike baki ta ce "Banza wai fushitake akan na ta6awa kishiyarta. Ki mutu mana aihar gida sai munzo mun yiwa Hanna tas sai dai atsiremu. Yarinya data rikita miki miji har ya kusa mutuwasbd ita k'iri-k'iri kina ganinta a cikin gidanki kinkasa yi mata komai, kema sai ta halaka ki takunna.Da Haisam ya fita ya nufo inda Hanna take a jinginea jikin mota tana kuka. Yasa hannu ya dafa bayantata juyo da sauri sai taga Haisam tayi murmushi tasahannu zata goge hawayenta idonta da sauri donkar yaga kuka take sai Haisam ya rike hannun ya ce"Kuka kikeyi?"Ta sake zubo da hawaye sharr ya ce "Hanna dainakuka kinji yi hkr, meye na kukan kuma me Hidatata isa ta sa ko kuma me zata hana karki damumutane ne daban-daban masu halaye daban- daban dole daman a sami 'yan zuga mararsa sonsuga ana zaman lafiya."Ya rumgemeta yana gogw mata hawaye.Sallamar Ramlaj ce tasa su duka suka dago Ramlahtayi ajiyar zcy ta ce "Kuka take yi?"Haisam ya ce "Lallashinta nake yi don bata ji dadin abunsa Hidaya tayi mata.Ramlah ta matso ya dafata ta ce "Hanna yi shirudaina kuka kada ki damu kinji ko, ina da hnklkuma nasan duk mai hnkl mai kaunata bazai banishawarar kar in zauna da kishiyata lfy ba.Kamar yadda Hjy ta fada mana dazu sai na toshe kunne na kema haka zaki sami kawaye ko 'yanuwanki masu zuga akan zamana dake sai muntoshe kunnuwanmu mu duka.Hdy kuma bata fahimce wacece kishiya ba kumameye kishi amma insha Allahu komai zai dai- daitatsakaninki da ita." Hanna ta gyada kai tada hannu ta goge idonta ta cenaji aunty Ramlah na gode. Haisam ya ce to yimurmushi sai mu san kin huce." Sai su duka ukunsuka tuntsire da dry.Hanna ta budewa Ramlah kofar mota, ta shiga tazauna sannan ta rufe itama ta bude kofar baya ta shiga ta zauna Haisam ya shiga ya kunna yaja sukatafi.Basu tsaya a ko'ina ba sai kofar gidansu mai gadine ya taso a guje yazo ya bude musu get Ya duka har k'asa ya mik'a gaisuwa. Haisam yawuce kai tsaye cikin gidan yaje ya tsaya a wajen daake ajiye motoci su duka suka bude kofofin motarsuka firfito. Haisam ya ce "To ai sai muje mu rakaHanna 6angarenta. Suka dunguma suka nufi 6angaren Hanna suna tafe suna hira har sukashiga. A babban falo suka zauna, Hanna ta shigakicin ta dauko lemon gwangwani guda 3 wandaaka yi shi da kwakwa ta dora akan dan faranti ta zota dora akan center tebur ta dauki daya ta bude tadurkusa har kasa ta mikawa Haisam ta dauko wani ta bude ta durkusa ya mikwa Ramlah sanna tadauko na karshen ta bude ta koma kan doguwarkujera kusa da Haisam ta zauna. Ramlah ma nadaya gefen nasa.Suna shan lemo suna kallon sittile tashar AfricanMagir wani Nigerian fim suke mai suna THE LAST UPPER, fim din yayi musu kyau mutuka sbd tsantsarsyy ce aka yi a ciki. Basu iya tashi daga kallon nanba sai da fim din ya k'are, karfe daya da rabi nadare.Haisam ya dubi agogo sai yayi sauri ya mike yadubi Ramlah ya ce "Anty ya kamata mu tafi haka kasa mu takurawa Hanna ko tana so taje ta kwantatayi bacci nasan yau da bana nan sai tafi sakewatayi ta juyi ita kadai a gado, Hanna ta kalle shi saitayi murmushi ta sunkuyar da kai.Ramla ta tuntsire da dariya ta ce "Sai kai yalla6ai kacika tsokana kana so dai ka cewa kanwata yau ta zama gauruwa da kyar in zata iya bacci.Hanna ba ta ce musu komai ba murmushi kawaitake yi, ta mike ta je ta kashe talabijin ta kwashegwagwanayen lemon da suka sha ta kai cikin.Ta fito ta iske Haisam a tsaye a tsakiyar falon Ramlana zaune hr yanzu. Hanna ta ce muje to in raka ku."Ramlah ta ce "Ai ke muka rako ko za'a yi rakiyarkura ne?"Barshi kanwata mu biyu ne fa."Haisam yayi murmushi cikin tsokana ya ce "Nasantsoro kike ji muje in rakaki sama ki kwanta." Hanna ta dan harare shi ta ce "Tsoron me?"Ni ba tsoro nake jiba ni yanzu ma kallo zanci gabadayi."Haisam ya ce,"Ai sama ma da kallo muje sama saikiyi kallon."Ya juya ya kalli Ramla ya ce "Ki jirani dan Allah minti 2 zan raka wanna gauruwar.Ramlah tayi dry ta ce "Ka cika tsokana, wacece iringauruwa bayan gata ga mijinta a kusa da ita.In kuma kana ganin baxata iya kwanciya ita kadaiba tazo muje mu kwana a 6angarena."Haisam ya ce"Hanna kin ji in baza ki iya kwana ba zo mu je mu baki daki daya ki kwana. Hanna tayi dry ta ce "AntyRamlah sai da safe babu komai zan iya kwana, batsoro nake ji ba." Ta wuce ta fara hawa samaHaisam ba biye da ita suna shiga daki Haisam yajawota ya rungumeta ya kalle ta ya ce "Fada mingaskiya yau zaki iya barci d bana nan ko baza ki iya ba?"Hanna ta sulale daga krjinsa ta nufi kofar bandakita juyo tayi masa fari da ido ta ce "Me yasa ka damuda sanin halin da zan shiga kai dai ba kana tare dauwargidanka ba." Haisam ya rike baki ya ce "Ahtambayata kike me yasa na damu da halinda zaki shiga, Hanna kin manta Haisam da Hanna?"Hanna tayi murmushi ta ce "to yi hkr tundatambaya kayi zan fada maka."Ta murda kofar bandaki ta shiga ta joyu ta dubiHaisam ta kashe ido ta ce "Daren yau zai zame munmarayen dare kwana dayan da baka nan zai zame min tamkar shekara 1 zan kagu gari ya waye wanidaren yayi domin ka kysanto gareni.Guzurin da zan baka shine zcyt tana gareka, ammakai bamzan so ka barmin zuciyarka gaba daya basai dai ka dan gutsuro min rabi, sbd idan ka banigaba daya zan shiga hakkin abokiyat zamana, tunda yanzy yaya Haisam bana Hanna bane itakadai. "Haisam yayi murmushi ya gyada kai ya cena gode Hanna knyi gaskiya kuma nayi farin ciki dakike sakani a kan hanyar adalci a tsakanin ku." Kiniya magana kin iya tsara zance mai dad'i a kanwatazan tafi da zucuyarki gaba daya amma gaskiya nima sai nayi da gaske zan iya bar miki rabinzuciyata sbd gaba dayanta tana gareki." Yana nufoinda Hanna take a hnkl ya karaso bakin kofar indatake tsayw suka zubawa juna ido me cike da Syytamkar kada su rabu da juna suke ji, can Haisam yanisa ya ce"Allah ya jarrabeni da wani ciwo mai tsanani wanda na rasa maganinsa, sai daga bayaAllah ya saukar min da maganin ciwon sbd damanko wacce cuta sai da aka saukar da maganintakafin a saukar da ita."Hanna ta kalle shi cikin mmk ta ce "Cuta! Wace irin cuta yayana?" Yayi murmushi ya juya yana tafiya a hankaki ya nufikofar fita.Hanna ta fito daga bandakin ta tsaya tana kallonsazuciyarta cike da zulumin kada ya tafi bai faita cemata abunda yake nufi da wannan kalamai nasaba. .Yasa hannu ya bude kofar dakin sannam ya joyuya dubeta yayi murmushi ya ce"Cutar ita ce tsananin sonki,maganinta kuma dana sami wacce nake son,Hanna na soki,ina sonki, kuma ba zan daina sonki bahar abada,sai da safe kiyi bacci lafiya."Ya fita ya jawo mata kofa ya rufe."Da bandaki zata shiga tayi wanka sai ta tsinci kantata nufi gado ta jawo filo ta kifa kanta tayi ruf da ciki tana murmushi zuciyarta cike da farin ciki dashaukin so.Ta sami soyayyar wanda take tsananin so.Wata dankararriyar soyayyar da take yiwa Haisamta dinga narkewa tana sake hawa kantaTa lumshe ido saita hango kyakkyawar fuskrsasai taji kamar muryasa nayi mata rada akunnuwanta. Haisaam na saukowa ya nufo inda ramlah takezauna yasa hannu ya tasheta tsaaye yaceuwargidana yi hkr kinsan bakuwa kwanan sabonwaje dole in dan tattaushe ta in bata hkr. Ramlaahtaji wani haushi ya tokare mata wuya ta dubeshisasai taga gaba 1 kalar danuwansa sun canja muryarsa ma ta canja ta tabbatar a cikin shaukin soyake. Lallai hanna ta caccako dandakarriyarrsoyayyar dake zcyrsa. Ta fusge jikinta dagahannuwansa ta huya masa baya cikin fushi tacehaka zaka ce mana inyi hkr kana can kuna takashew juna zcy gashi nan idinka duk ya narke kana wni kashe murya to in har kwana 10 danabaka baiyi maka ba ka koma sama ni inyi tfy ta.Kafin ta rufe bakinta haisam ya jwota jikinsa yarungumeta tsam a kirjinsa yana cewa haba antyrmlah ya ina yabanki salla zaki kasa alwalla karfa kibata rawarki da tsalle mana, babu wani kashewa juna zuciya da mukayi cewa nayi ta tattofa addu'a akowcce kusurwar daki shikenan fa abinda nacemata, wnn idon nawa kuwa da kika ga ya zamahaka barci ne muryata kuwa mura nake. Taharareshi tace naga alama mura ce ta kama kaamma a yanzu daka hau sama ko? Haisam ya kyalkyale da dry yace naga alama yau ramlah sokike ki rikece mun, yau rigima kikeji zo in goyakimu tafi .bata yi niyyar yin dariya ba dariyar tasubuce mata ta kyalkyale da dry tace kyaleni ni bawani goyo. Haisam ya jawota da karfi yace wai dolesai ya goyata. Ramlah tace to tsuguna in hau da kain. Haisam ya tsugunno, ralmah ta haye bayansasnn ya fito ya lalubo mukulli a aljihunsa ya kulle tabaya,Ramlah tace ah ya zaka kulleta a ciki. Haisamyace da mukullinta ai a wajenta in zata bude saitabude ta ciki. Ya fara tfy ya nufi bangaren ramlah canya tsaya ck. Tsakiyr hnya y ce wai wai nauyi saukohaka hoyon ya isa ki karasa da kfrki. Kinsan fabake kadai bace. Ramlah ta harari keyarsa tace in bani kadai bace ni dawa nake? Yayi dry yace kedadan cikin ki mana. Ta dan ja kunnensa tace dagafada maka mgn harka fara yayatu aka to saura kadinga fada har kowa yasan ina da ciki. Kuma bazansauka ba sai ka kaini har cikin gida kn gadofurnishment ne daman kumaza idan kukayi sabuwaramarya saidai uwar gidan ta toshekunnuwanta ta rufe idanuwanta ta dainakallonkusbd wnn zumudin sai kunyi shi. Yrny tace ba tsorotakeji ba wai kai a dole sai ka rakata tsoro takeji kowaya saka oho. Ramlah na baya tana yiwa haisamtsiya shi kuma yna ta tfy yana dry a ciki. Har kan gado yakai ramlah snn ta sauko ta shiga bandakihaisam kuma ya mike aka gado yana nishi waikshin bayansa ya kusa karyewa sbd nauyin ramlahda dan cikinta ramlah na jiyoshi tana wnka tana drytanacewa ka santa. Bayan ramlah ta fito sai haisamya tashi ya shiga shima yayi wanka ya fito daure da tawul ajikinsa ko kayansa baisa ba ramlah ta faradane bayansa tace ya kaita kicin zata dauko ruwansha, nan dai suka hau kokawa haism yacebazigoya ta ba itama daman tsokanar sa take bakishirw takeji ba suka runtuma kan luntsumemangdon dakemalale a tsakyar dakin suka cakuda suka ya mutse junansu yyin da kokawa t komasumbatar juna, da shafa juna da rungume juna.Haisam da ramlah sun farantawa junansu matuka acikin daren yau.Kamar ydda hanna da haisam suke kaiw ramlahziyara byn sallar azahar yau ramlah dahaisam sundungumo bangaren hnn don suci bincin rana dadare a wajenta daman sunyi mata waya sun sanarmata da kunkunta yazo tana bye dashi tanakoyonduk yadda yakeyin abinci irin na yn gayu na zamani don ta koya ta iya, ta hutar da masuiki tadinga yi da kanta. Hakahanna da ramlah damijinsusuka kasance cikin farinciki da kwanciyar hnkl,zaman lfy da kaunar juna. Kwanci tashi hanna tayi wata guda da rabi a gidanmijinta. Misalin karfe 5 nayamma haisam damatansa suna zaune a falon ramlah suna hra wasada dry. Haisam yace gsky na gaji da bin dakunankuduk mai girki tazo ta sameni a bangarena kullum nikenan cikin rrarraba kayana sai ina bangaren ramlag na tashi zan dauko agogona sai in tunayana bangaren hanna idan na tashi zan daukogilas dina sai in tuna na barshi a dakin ramlahshekaranjiya ma sai rigar hanna na saka ta barcisbd ashe da mai wanki da guga ya wanke yafitarmin da kyn barcin gaba daya ya hada min kayayyakina na bangare na. To nagaji kowaccetahado min nawa bangaren, abinci ma duk maigirki tasa a dafo azo ajiye akan teburin cin abincinasnn kowacce tzo mu hadu muci. Ramlah da hannasuka kece da dry suna cewa kaidin dai ka dingazuwa tunda haka ka farayi. Haisam na cewa naki wayon ai yanxu na fara gane wayo kuke mun.Hayaniya da dry da sukeyi ita ta hana suji na dannakararrawa ana ta kwankwasakofa. Can hanna tajitace ana danna kararrawa fa. Ta mike da sauri tazota bude. Wasu mata neguda 3 hadaddun 'yangayumasu ji da kudi kallo 1 zaka yiwa dukkanin su ka gane 'yan hutu ne suna da kyau kumadukkaninsu.Mace daya a cikinsu tana da tsohon ciki ko yauko gobe. Hanna tayi musumurmushi gami da yimusu sannu da zuwa. Bata ishesu kallo ba balle suamsa mata kaitsaye suka wuto cikin gidan. Ta bisuda kallo zcyr ta cike da mmkn meye haka kuma lfydaga zuwansu su haubata rai da harare2. Tasake kallonme cikin don tana yi mata kallon sani, is canta tuno ashe hadiya ce matar yaya habib nowonder hanna ta fada a ranta. Ta tura kofa ta rufeta nufo indasuka zzzune a sanyaye cike da fargabatasan ko tagaishe su baza su amsaba. Ta bari sukagama gaiswa da hisam snn ta gaishesu. Kokontonta yazamagsky ai basu amsa mata ba saima wata harara da suka sakar matadukkaninsu.nan fa aka hau kallon kallo tsakaninhaisam da ramlag da hanna da kuma wandannanbaki. Hidaya ta yamutse fuska tace aisha sulaiman,hauwa mamman kuzomu koma wancan falon mu zauna mun isa muzomu zauna a tsakiyar amarya daango. Aisha taxe da kuma uwargidansu ramlah kinmanta baki fada ba. Hauwa mamman tace oh hakane fa baku gani bama amaryar sai wani hararar mutakeyi lalli zuwa gidanki ramlah nan gaba sai munshirya, to bngarenki ma 'yan uwanki da kawayenki basu isa suzo ba ashe tota biyoki ta biyo mijinta.Suka mike suka nufi daya falon. Ramlah ta rasa ta cewa ta bisu da kallo kawai cantanisa ta juyo ta dubi haisam wanda yayi shiruyanakallon talabijin amma kallo 1 zaka yiwa fuskarsakasan a bacin rai yake. Hanna kuwa ta sukuyar dakai kasa hakika nan da wasu 'yan dakikai zata farazubar da hawaye. Ramlah tace yallabai wai me su hadiya suke nema ne dani, yaya suke so nayi?yasahnnu ya dakatrdaramlah yaceyi shirukarma kibata bakinki barni dasu jeki gurinsu bakinki ne. Can ramlag ta yukunra ta mike ta nufikicin tashaidawa kuku da sauran masu hidimarta su hadujuices da snacks su kawowa bakinta, tazo falon dakawayenta suke suka fara cafcafkewa suna hira. Haisam ya kurawa hanna ido yana kallonta cn tadago ta dube shi saita daure dakyar ta kirkiro wanidab bushashan murmushitace yauwa ko kefa,meye abun damuwarki? Kidaina damun kankiakan irin wadannan yan matsalol kinsan dai ba za asake irin tataburzar da akayi a kazaure ba ko? Ba za'ayi irin yadda kikayi dasujuwairiyyaba sahabi,principal , yaya habib da rauda ba ko? To dukwadancan basuzamar mun matsala ba wajenwargazasu balle su hidaya, zanyi maganinsu inshaAllah kallonsu nakeyi tukunna wata rana ko kudiaka basu akace suzo gidan nan su yadr mikida mgn baza suyi ba. Hanna ta nisa ta girgiza kai ta ceyaya da zakaji shawarata ka tamakeni ka kyalesudan Allah kome zasu yi min kuma komezasu cekabar su ni na saba da duk irin wadannantsangwamar tuntuni a ryw ta. Tsorona dayakadayau da gobe suna zuga anty ramlah tun bata dauka har tazo ta fara dauka zamanmu yazo yaki dadi.Haisam ya girgiza kai yace haba hanna I tun dagaranar da muka sakr haduwa ranar da akace mikina rasu kija fitodaga daki kika ganni na gankikikayimurmushi hakika nasan farin cikin da kikaji aranar bazai musultu ba daki ganni a raye ban mutu ba, to dayardan Allah tun daga ranar har karshenrywr ki kin dinga farin ciki kenan, kin rabu dadamuwa da tsangwama insha Allahu. Hanna tayimurmushi tace nagode mai gidana, to mma inagudun zcyr ka da zafin fushinka irin na kazaure.Haisam yayi dry yace tunda na same ki ai komaima a sauki zan ringa daukarsa na daina fushidayawa my love suka sakarwa juna murmushi. Yace bude dibaidar can ki dauko min jarida zankaranta, ta mike a nutse ta dauko msa tazo tadurkusa ta mika masa tazo kusa dashi ta zauna, yana karatu ita kuma tana kallon talabijin. Wayardake dore akan tebur (landline) tayi ruri. Ramlahtasa Hannu ta dauka muryar kawarta taji mrsblessing ma'aikaciyar filin jirgi a abj bayan sungaisa saita sanar mata da cewa bizar hanna dahaisam ta fito don haka su zauna cikin shiri nan da kwana 2 jirgi zai daga zuwa london daga abj.Ramlah tayi mata gdy sukayi sallama ta ajiye wayar.Tace da kawayenta ta na zuwa. Ta mike ta nufifalon da haisam suke zaune ta fizge jaridar da takehannunsa yana karantawa tayi dry tace albishirnazo inyi muku bizar ku ta tfy kasashe 5 ta fito nan da kwana 2 zaku tashi london daga abj. Haisamyayi dry yace to madallah ramlahta ai shiyasa banawasa da sha'anin ki, yanxu koh sati 2 ba'ayi ba dazuwa abj neman mana visa har an samu. Ramlahtayi murmushi tace haba dan neman bizar, ai koshatar jirgi kake nema cikin kwana 1 zansa a nemo maka sbd kwayena wajen su 3 ne koh banje bainna yimusu waya zasu yimin duk abinda nakebukata, balle in tashi naje abj da kaina kasan dolesu zage dantse su nemo min biza da wuri sun sanba karamin sauri nakeyiba. Hanna dai sai murmushitakeyi. Tace anty n gdy mukeyi fa sannu da kokari. Ramlah ta kalleta tayi dry tace in banyi muku ba wazaniyi babu komai fatan alheri nake muku kuje lfyku dawo lfy ku samu lfy.Hanna da haisam suka hada baki sukace amin.Ramlh ta juya ta nufi wajen kawayenta wanda sukasaka kunne suna sauraron abinda suke fada. Saisuka sake jin haushin ramlah kowacce ta rike bakidon mmk wata na salati wata na tsaki. Ramlah takaraso tana murmushi ta zauna. Ta daga ido taga gaba 1 su hararanta sukeyi. Tayi mmk matukakafin tace wani abu sai taji an turo kofa gami da yinsallama , mai gadin su ne yazo ya durkusa a gabanramlah ya gaishe ta yace daga gidan gwamnati neakaturo wasu mata guda 2 wurin hjy hanna na turasu bangarenta sunje su ce a kulle yake shine nace bari na duba ta nan dan banga fitar ta ba ko tananan? Ramlah tce eh tana nan kace musu tana zuw.Ya mike yana gdy ya fita, ramlah ta kwallawa hannakira. Cikin ladabi hanna ta amsa ta taso tazo wajenramlah. Ramlah tace baki kikayi maybe nusaiba ceta aiko su suna waje inji maigadi. Hanna tayi murmushi tace toh bari naje nagode. Ta wuce tanufi kofar fita su duka suka bita da kallo. Watadandatsatsiyar shadda ce a jikinta pink colour anyimata surfani da design me kyau a zani da rigar dadankwali wato (ready made). Hanna tayi kyaumatuka. Lallausan gashinta ne har tsakiyar bayanta ta sake shi byn ta daure da pink din ribbon. Aisha sulaiman tce turkashi, hauwa mamman tacerigijigafji inji masu iya mgn. Hidaya tace wani kayasai amale. Ramlah ta dube su dukansu tace ah waniyare kukeyi bana jin ku? Hidaya tace yaren hausamukeyi yi mana. Ramlah tace ban fahimce ku ba.Aisha sulaiman tace turkashinace. Hauwa tace rigijigafji, Hidaya kuma tace wani kaya sai amalegaba daya abu 1 muke nufi gaba 1muna mgn neakan babban aiki,Ramlh cikin mmk tce wanne irin aiki kuma?Aisha sulaiman tace hidaya ku fada mata danniidan na cika yawan mgn sai jinina ya hau sbdtakaici. Hidaya ta nisa tace Ramlah, ramlah saunawa na kira sunanki? Kn bani kunya, kuma kinbani mmk, wai shin meke damun ki ne? Ramlah meyasa kika zama makauniya alhali kina gani daidanuwanta guda 2.kin zama wawiya alhali kina dawayo.kin zama kamar baki san abinda kikeyi baalhali kina sane. Ina miki fargaban ranar da zakizokina da na sani. Kina zubar da hawaye daidanuwanki. Ramlah taji gabanta ya fadi ta fada cikin rudani wai meke faruwa ne? Me kuke nufi?Don Allah ku fada mun abunda nayi yadda zangane na kasa fahimtar ku. Hauwa mamman tace abunda muke nufi shinekinyi kuskure, kinyi sake, kin dau abinda saukialhali ba mai sauki bane. Ramlah yanzu kece kikasamarwa mijinki bizar da zai fita da amaryasa sujesu shakata a kasashen waje ke kina gida a zaune.Wai shin ke me kika dauki kishiya ne? Karfa ki dauki hanna karamar yrny wacce batawayeba, ki dauka baza ta bude idonta ba tayi mikirashin mutunci a gidan nan ba. Dubi yadda hannata zama a cikin wata 2 ta goge tayi kyau tamkarwata baturiya kina zaune . Na 1 tana da kyau har tafiki, na 2 ta iya kissa da kissina da iya mgn ga ladabinmunafurci. Da sannu zata tafi da zcyr mijintada iyayensa da duk dangins kina zaune bude dabaki, aisha tace ah to mudai mun zo ne mu fadamiki gsky kin sakarwa kishiyarki da yawa dubakiga falonki shekara 2 kuna tare da haisam bakudauki hoto baku 2 kn lika a falonki sai zuwan hanna kuka hadu ku 3 kuka dauki hoto kalli hotonko kishiba kyaji kika lika hoton kishiya a falonki.gaba 1 kin canja ramlah kamar ba keba. Ki tsaregirmanki ko ganinki tayi sai gabanta ya fadikaryata nan gaba tace zata waye tace ta takaki.Shima dole yaji shakkarki ba zai sake da ita ba.Haka rannan naji ance har gidanku kika dauketakika kuka yini, lallai kishiya ta zama kawa. Hauwa mamman tacewlh ni duk ranar da ibrahim mijina yatarki aure daga shi har amaryar sai na babbakesuaina fada masa. Bai isa ba shi da kansa yanzu yakecemun ko bashi mace akayi ba zai karba ba, tokingani namiji zumane sai an babbaka masa wuta.Hidaya ta yamutse fuska tace ke kin fadwa mijinki mairin hukuncin da zaki dauka idan yayi aure toniban fada masa bama matakin da zan dauka ammashi da kansa ya sanni ko a hanya muna tare bai isaya daga ido ya kalli mace ba balleyayi min zncenaure a wsa ranar saidai ya kwana a bakin get dankulle kofata nakeyi in kyaleshi balle yayi dare. Aisha suliman tace muktar mijina ai ya taba tarkaraure ramlah kin mantada irin tashin hnkl da mukayi ba shiri ya fasa to haka akeyi muddin kika yisakw sakwa za'ayi babu ke. Tunda ta riga ta shigoynzu ke abunda ya kamace ki ramlah ki iyatakunki. Kishiya ba abar yarda bace kada ki barta ta sake ta baje ta baza kayanta tayi kane kane tamallake miki miji ta mallake ki. Hidaya tace waikishiyar ma data sake daita wayayyiya,kyakykyawa irin hanna, ai irinsu hanna bai kamataki sake ba sbd duk wani da namiji burinsa ya samimace kamar hanna balle wanda ya aureta dole ya rikice ya mace mata ke kuma kina zaune a gefe. Kiyidai tnn ramlah akan nasihar da mukayi miki dongsky mu mun hango miki abunda baki hango ba.Ramlah tayi shiru kanta a sunkuye a kasa jikintayayi sanyi sai yanzu ta dago ta dubesu tayi ajiyarzcy tace naji abinda kuka fadamin nagode. Takirkiro wani laujajjan murmushi dakyar tacehidaya, Aisha da hauw kawayena kenan. Intambaye ku mana shin nana Aisha (RT) matar manzon Allah (S A W) kishiyoyintaa nawane? Matrannabi 9 ya aura suka zauna tare. Kun manta indaAllah (S W T) ya umurci maza dasu auri matayebibbiyu,ko uku3 ko hur hudu4 idan sunga bazasuyi adalciba su auri 1. To ashe ba haisam bane yakirkiro auren mata 2 don ya cusguna min ko don ya bata mun rai shi da amaryasa. Hakika na rikiwnn hadisin da Annabi Muhammad (S A W) yakecewa imanin daya bazai cika ba har sai ya sowadan uwansa abunda ya sowa kansa. Su duka sukace Allah Akbar. Yayin da dukkaninsu suka tattaroda hnkln su ga sauraren ramlah. Taci gaba da cewa kuma rai yanason mai kyautata masa. Hanna tanakyautata mun, hanna tana girmamani haka haisamyana farantamun. Kullum addu'a nake Allah yazaba mana abinda yafi alheri tsakaninka da haisam.Alherin da Allah ya zabar mana shine ya kawohanna. Tsnanin kishin da nake dashi da kin hanna da nake yi da sai Allah ya yaye min a raina najiinason zama da ita musamman dana yaba da hnklnta. Ni a yanzu da kuka ganni bani da wani buri aduniyr sai inyi biyayya gamijina in shiga aljannahkuma in kiyaye kadaincuci bokiyar zamata mugama lfy sbd duniyar nawa take yanzu kananan anjima babu kai ka mutu ka kuma tafi har abada.Daman yanzu a wnn zamanin da muke duk wanimai hkr shine abun zagi an dauke shi wawa mararhnkl kamar yadda a yanzu kuke daukata to gskyba haka bane nasan abunda nakeyi,Ina kuma jin dadin rywr aure na a yanzu fiyedarywr aurena a da. Kuna murna kuna jin dadi a zcyyinku harma kuna furtawa da bakinku kunatunkaho da takama kun hana mazajen ku aurekuma sun hanu. Sbd suna tsoronku kuma kun isa,nice marar wayo dana bar mijina ya kara aure har muke zaune lfy to alhmdl naji dadi. Kuyi hkr bawaina gwaleku bane, kuma bawai ban gode muku banaji dadi da kuka hango abunda zai cuceni kukasanar dani, saidai ina ganin baku fahimceni babaku kuma fahimci wacece kishiya ba da zamantare. Saimuke kallon kallo ni da ku ma'ana kuma mun kallon inama injiabunda kuke cemun. Ni kumaina hango muku wata babbar illa akan mazankuhar nake cewa inama zaku yarjewa mazajenku suyiaure kamar yadda haisam ya kar aure ku zauna lfyyafi kwanciyar hnkl. Hidaya tasa hannu ta dakatar da ramla tace karmaki fara hango mana inama mazajrn mu su kara auremu zauna lfy wanne irin zaman lfy anyi manakishiya ai lkcn ma zama zai hrgitse. Aisha tace kedai ramlh da Allah yayi miki zcy irin ta matansahbbai kinji dadi kinason kishiyarki amma mu babu sauki idan akayi mana kishiya. Su duka sukakyakya ce da dry suna tafawa. Huwa tace kishiya,kishiya ramlah kinji yadda nakeji kuwa idan nagaanyi kishiya a makabtnmu ma balle a cikin gidanaai har abada bazan ydda da kishiya abokiyar zamabace idan kuwa ya kuskura yayimin karshen zamana yazo a gidan kuma suma sun rasakwanciyar hnkl a zamansu lallai ramlah baki sankishi ba. Ramlah tayi murmushi ta gyada kai tace.Hauwa kin tabo wani kyakykyawan misali danakeso in baku kince daga ranar da mijinki yayiure kin bar gidansa, a matsayinki na yar shekara 25 kina nufin idan kika rabu da mjinki kin rabu dayin rabu da yin aure kenan. Rywr ki har abad?Hauwa mamman tayi shiru can tace sai in sami waniin aura. Ramlah tace saurayi ko baxawari? Tundake bazawara ce kinga saurayi ba zai zo nemanaurenki ba sai dai wani ikon Allah. Masu mata ne zasu dinga zuwa neman aurenki to su matan dazaki auri mazan su su ba mutane bane da zasukyale mijinsu ya aureki? Kinga ko yanzu kin barsunna don baki sowa dan uwanki abunda da kikasowa kanki ba kin auri mijin wata. To ai haka neabunda nake nufi da inama zaku yarjewa mazanku su kara aure yafi kwanciyr hnkl shine na dadeinason in fada muku abunda yake raina na rasa taina zan kara fada muku fahimta amma yanzu zanfada muku tunda yanzu mun ku fahimceni kamaryadda na fahimce ku. Hidaya tayi dry tace ai yanxura'ayoyin mu iya bambanta aminiyata kin baude daga cikin mu kinbi wata baudadiyar hanya tagushewar ganewa mun ksa gane kanku. Yayagashi kiri2 ana cutarki kowa yana gani kince bacuta bace, mufa muna nan akan bakarmu kumakullum zmuci gaba da fada miki har sai kin gane.Ramlah tayi dan murmushi ta mike tsaye taje ta rage muryar talabijin din dake kunne ta dawo tazauna ta dubi fuskokinsu dukkansu sai fara'a sukealamar ma dry take basu. Sai itama suka bata dry takyalkyale da dry suma sukayi dry, hidaya tace aibabu abunda xaki fada mana ramlah kema kyayidry sbd ba'a haiyacinki kike ba tuntuni na fada miki wnn kishiyar taki ta gama da ke.ramlah ta nisa tace ina da bun cewa shiyasa mahar nake dry. tace inada abun cewa ne shiyasa mahar nake dry. ku gafarce ni hauwa mamman barikijiabunda baki sani ba gafarce ni hauwa mammanbari kiji abunda baki. saniba game da mijinki ammainaso ki nutsu kafin ki yanke hukunci dole ne tasa zan fada miki yanzu ma don kawai ki yarda dabayanin da nakeso in wayar muku d kai aka kukakasaganewa kinsan amira nsir? hauwa mamman tazabura ta rike kirji tace ramlah ina kika san amiranasir? ai ita ce tacacciyar 'yar iskar yrnyr dana fadamiki 'yar minna ce take yiwa mijina waya tana sonsa amma ban fada miki sunanta ba, nima saidaga baya na binciko sunanta amma ai yanzu tarabu dashi ko hanyar da yabi dashi ko hanyar dayabi ma ta daina bi. ramlah tayi murmushi tace hakaya fada miki to ga irinta nan abunda nake fadamuku kun kasa ganewa. da mace tasa mijinta a wanihali na bin matan banza gara ma kabarshi yayiauren, hauwa mamman ta gyara zama ta marairaicetace ralmah meke faruwa ne gabana faduwa yakefadamun gsky. ramlah ta nisa tace gsky bsu.rabuba kuma sau 2 muna haduwa dasu a londonni da haisam duk fitar da yake da ita yake fita ina amfanin haka bayan uwar dukiyar da yake turamata. ai ba'a london kadai ba jama'ada ywa sunsani ba na tayi miki kallon wawiya. kinga da irinwnn harkar gara ma ace ya auro miki ita cikin gidakun zauna tare kamar ni da hanna dai. hauwamamman ta dora hannu aka ta tsala kuka. aisha sulaiman na rirriketa kuka take tana cewa wlhramlah gara ke daya auro miki hanna ashe, yanzuhaka ibrahim zai yimun na shiga3 yanzu ramlahyaya zanyi? ashe kowa ya sani baku fda min ba?ramlah ta juya ta kalli aisha sulaiman tace ke kumada kike ganin kin hana muktar aure ya hanu to kece baki sani ba yna nan tared yyny kuma yakaikudun auren a boye, yana gina mata gida a abj canzai kaita inda yake aiki ai ayi auren rufe karki sani.Hidaya ko b kwar yrnyr bace take fda mana taredake ba? to ashe ni da haisam ya sanar danigawacce yake so ya aura sai in msa butulciince bazamu zauna lfy ba. aisha sulaiman ta hau cire mayafitana fizge dankwli tace ramlah da gske kike ko dawasa na shiga3 na lalace. ramlah tace baki lalace ba aisha darasi ne akanku domin kusan kara aurefadar Allah ce babu wcce ta isa ta soke tace baza ayiba. hidaya ta rike baki tace kai dny abun tsororamlh na fara tsorata da al'amuran maza yanzu, nikuma me habib yakeyi bansani ba? ramlah tayimurmushi tace ciki gareki hidaya bai kamata a fda miki mgnr da zata tayar miki da hnklba hidaya tazabura tace in akwai ni fdamun ramlah karki ciamanata babu wani abunda zai sameni don inadaciki fadamin gsky. tana rufe bakinta sai taga haismakanta yamiko mata wani kati. ramlah tayi sauritasa hannu zata fuzge sai hidaya tayi sauri ta fuzge tna karatawa taji kamar an daba matawukaakirjinta. katin da wasa habin bai taba fada mata basbd yasan tsananin kishinta shi kuma so yake yakara aure donhaka ya kwabi duk. wanda yasanzaiyi aure da kada ya fadawa hidya yace zaiyi aure.hidaya ta rike hanuu haisam gam ta rusa kuk tana cewa wlh saika karbo min takardata a wajenyayanka na fasa auren. haisam ya hau dariya yanacewa ni suwa ke da kika isa da mijinki jeki kisameshi. kiyi hkr kawai ki zauna ga tsohon cikiga'ya'ya ina zki kaisu. hidaya zma da kishiyayasame ki sai ki hkr daina ma kuka.....2⃣1⃣ juya yadubi hauwa da aisha kowacce tamkarzararriya abun daya dameta ya dameta. babusallama kowacce t zari gyalenta ta fita. ramlahnacewa ku dawo kubari a gama girki mana, ina babuwacce ta kalleta bare susan me take cewa. direbanhiday ne ya kawosu,mota kawai suka ta fada. ramlah ta bisu tana rokarsu don Allah su kwantarda hnkln su su bari zcyrsu ta huce kafin su yankehukunci.karsu yanke hukuncicikin fushi subikomai a hnkl. basu iya ko mgnba sbdmakkinbakincikiko wacce sauri tke burinta taganta a gida tyi arba da munafikin mujinta mace amana, suka jamota suka tafi. haisam ya jwohannunta suka shiga gida su duka dry ce tahanasu yin mhn. sunyi minti 15 suna drysuyi suhuta su sake tonowa su kwashe da dry haka daisukayi tayi. haisam yace ai duk hirar da kukeyiinajinku nayishiru ban tank musu ba sbd naji kina basu amsar data dace. hakika ramlah kin birgenikin cika mai hnkl da tnn da kaifin basira. kinburgeni daywa da baki dauki shawarsu baamsoshin da kika basu yayi daidai datambayoyinsu. nasan yaya habib zaiyi fada don men fadwa hidaya toko me zaiyi yayi ni dai na riga na gama fada sbd ta cika min ciki tun rannan nakecike da ita. wai shin ina ruwansu da gidan wata?banda gulma irin ta mata inake ina matsalar wanigida ita wacce aka yiwa kishiyar tace babu komaiku kun dage kunce akwai komai, suna bani mmkwlh. ya jwo ramlah ya rungumeta yace ynzu haka wani sonki ne na hnkl ya kara lullubeni.ramlh talumshe ido tace na gode da yawa.. Zaharaddeen Shomar Whatsapp 08168575100 GANGARJIKINSA NA AURA 3 Part 3 Posted by ANaM Dorayi on 06:05 PM, 30-Apr-15 Under: Gangarjikinsa ta Aura Ramlh talumshe ido tace na gode da yawa.Tana rufe bakinta Hanna ce ta turo k'ofa ta shigogami da yin sallama tayi turus ta tsaya cak don bazata iya k'araso inda suke tsaye a rumgume dajuna. Tayi kamar ta bud'e k'ofa ta fita sai dai tadaure ta had'iye mak'ak'in kishin daya taso mata, nauyi da kunyarsu ta kamata. Haisam ya sakiRamlah daga rumgumewar da yayi mata. Ya dubiHanna wacce kanta ke sunkuye a k'asa ya ce "Meyekika tsaya a xan ki k'araso mana."Tayi murmushi kawai ta nufo inda suke ta dubiagogon dake daure a hannunta ta ce "Zanje inyi alwalla magruba tayi."Sai su duka suka nufi band'aki dn yin alwalla.Bayan sun yi jam'i sun idar sai suka zazzauna akanabin sallarsu kowacce ta bud'e Alk'ur'aninta tanakarantawa.Har lkcn sallar isha'i, yayi suka tashi Haisam na jansu suka yi jam'i suka yi sallar ishai'.Bayan sun idar suka yi addu'o'in su suka shafa.Kafin su idar masu aiki sun gama jera musu abincikala-kala akan teburin cin abinci.Kai tsaye suka nufi dinning table, Ramlah ta farazuzzubuwa a kowanne plate. Ta zuzzuba lemo (juice) a kowanne kofi ta koma tazauna kowa ya fara cin nasa.Suka dau lkc mai tsawo babu wanda yayi maganaHaisam ya dubi Ramlah ya juya ya dubi Hanna ya ce"Yau abincin yayi dad'i sosai ko mgn kun kasa yi."Su duka suka yi dry. Hanna tayi masa lallausan kallo ta ce "Ka cika nemnmgn kaine fa kace mu daina mgn idan muna cinabinci yanzu km kace mun kasa mgn."Ramla ta ce "Ai dokar da yasa shi tafi effecting sbdyalla6ai baka iya zama minti 10 ba kayi tsokanaba." Haisam ya ce "Kullum dai ku bakinku d'aya neabunda yaya ta ce haka k'anwa take cewa hakaabunda k'anwar ta ce yayar sai ta ce hk ne,k'anwata babu mai bin bayana a cikinku ko toshikenan tunda had'emun kai kuke nima zan samome shigarmun.In yi k'anwa. Hanna ta harari Haisam ta ce wace irink'anwa kuma?" Haisam ya ce "Kishiya mana kungasai ayi bibbiyu kenan ku biyu nima ni da ita sai tadinga shigar mun,"Ramla ta tuntseri da dry ta ce "K'anwata ke yake tsokana ai na gaya miki shi daiyayi tsokana yaji dad'i."Haisam yasa hannu yana shafar kumatunta Hannaya ce "Ke da wasa nake ye miki.Ai na gama aure a rayuwata insha Allah.Kuma inajin dad'in wannan had'in kan da kuke mun.Tsokana nake yi ina ni ina wani k'ara aure har alahira na gama k'arin aure.Ramla uwar gidana Hamma amaryata hr abada."Su duka suka yi dry."Ya ce "Allah da gaske nake, ko kunga nayi muku kama da wanda zai k'ara aure ku kalleni tsaf anutse ku k'are mun kallo."Suka tsuntsire da dry dukkaninsu hr Haisam d'in.Ramla ta ce "Hanna dai dry kawai take yi bata cekomai ba kai kayi kid'anka kayi rawarka."Haisam ya ce "Ni yanzu abunda yake gabana shine inga dukkanin ku na baku jari kowacce ta kamasana'ar ta kanta, Ramla yanzu misali idan aka bakijari me kike da sha'awar bud'ewa "Ramla ta ajiyekofin dake hannunta tayi fari da d ido ta ce "Ni agaskiya ina da burin bud'e kantin sayar da kayanSenegal na mata da maza sabba inyi wani kant wanda zan singa sayar da takalma na k'asar wajetsadaddu na mata da maza da yara." "Haisam ya ce "To ya isa haka anty Ramla naga sokike ki bud'e kantina daban-daban.Idan na kyaleki saiki k'irgo min guda goma biyuma sun isa.Kefa amrya ta?""Hanna ta narairaice ido ta ce "Ni dai burina da ace ina da kud'i makaranta Islamiyya zan bud'e damasallaci da rijiyoyi da bishiyoyi zan shuka inceAllah ya kai ldn kabarin iyayena da suka rigamugidan gaskiya."Haisam ya ce "Allah sarki shikenan?"Hanna ta zubo da hawaye daya cika mata ido ta ce "Shikenan burina."Haisam yasa hannu ya share mata hawaye ya ce"Kar kiyi kuka ajiye wannan a gege za'ayi inshaAllah a sana'a me kike da burin yi?" Hanna ta d'anyi murmushi ta ce ina so in bud'ek'aton kanti (super market) a kusa da nan kuma inbud'e wani d'an ofis na taimakawa marayun yara." Haisam ya ce "Duk kun za6i sana'o'i masu kyau,nima bari in fad'a muku tawa sana'ar a Abuja nagina wani katafaren wajen k'erarre, k'ayatacce maikyaun gaske nan da wata 2 za'a kawo min moticidaga Germany zan fara sayarwa idan mun dawodaga tafiya in Allah ya kaimu zan kaiku ku gano wajen." Hanna da Ramlah suka yi murmushi dukkansusuka kuma tayashi munra da fatan alheri." Haisam ya ce "Na gode sai dai kuma na kasa tunosunan da zan sakawa wajen misali Hanna da zakibud'e super makeket wanne suna kike so kisawawajen?"Kema Ramla yaya sunan boutik d'inki da zaki bud'eku d'an bani satar amsa sai insan wanne suna zan sawa wajen sayar da motocina." *Ramlah tayi dariya ta ce "Aini sunanka zansawawajena."*"Haisam Senegalise boutique."Haisam ta girgiza kai ya ce"Baiyi ba,"Kefa?" *Hanna ta yi d'an murmushi ta ce "Sunanka danaAuntyna Ramlah zansa "HAIRAM SUPER MARKET." *Haisam ya ce "Hairam ke kuma laifin me kikayi dakika cire sunanki k'ara Hanna akan hairam d'in saiyafi dad'i.Hanna tayi dariya ta ce"HAIRAMHANA SUPER MARKET.! *Haisam da Ramlah suka had'a baki suka mai-maita. HAIRAMHANAH sunan yayi dad'i gaskiya.Haisam ya ce "To da nawa dana aunty Ramla danaamaryata Hanna duka sunan d'aya ne, kunga *HAIRAMHANAH Super Market."*HAIRAMHANAH Senegalise boutik'ue,*HAIRAMHANAH Motors da dai sauransu.Yanzu kowaccenku zan bud'e mata account zanzuba muku miliyan hamsin-hamshin ku fara jarindashi kafin nan gaba in k'ak'k'ara muku,Nima ina cikin zamana Babn mu ya kira mu ya cetunda munyi hankali kowanne mu ga takardunhannayen jari da ya dinga zuba mana tun munayara a bankunan k'asashe daban- daban dabankunan nan k'asa Nigeria." Kud'ad'e masi yawa sun taru shekaru da yawabamu ta6a kar6a ba ya ce muje mu kula da kanmuda iyalinmu. Sannan an biyani kud'in kwangilar da nayi tamiliyan d'ari 2.Sai naga ya dace nima inzo in bawa kowacce jari tajuya da kanta don tayi hidimomin gabanta ba saikun jirani ba kullum ina d'an san muku d'an nakashewa ba." *Ramlah ta rik'e baki ta ce,"Yalla6ai miliyan hamsin-hamshin fa ka ce?" *Hanna ma ta ce fifty millions?" *Haisam ya ce "Miliuan hamsin kowaccenku."*Hanna da Ramla suka zo suka durk'usa a gabansasuka yi ta godiya."Yasa hannu ya tashe su tsaye ya ce babu komai shiba sai sun gode masa ba.*Hanna ta nufi k'ofar fita ba tare data yiwa kowa sallama ba a tunaninsu kicin zata shiga sai suka gata bud'e k'ofar fita ta fice da alama kuma kuka takeyi. *Haisam da Ramlah suka hau kallo, Haisam ya ce"Ina ita kuma wannan zata je babu sallama." *Ramlah ta ce "Ka bita ka gani, ina jin gidanta tafida almar kuka take yi."*Haisam ya ce "Ai kukan ma ta tafi zata yi ya ishetadomin gwanar kuka ce na tabbata ta tunamaraicinta na zata ga kud'in bashi da amfani awajenta sbd sunzo lkcn da babu mahaifanta." *Ramlah ta girgiza kai ta ce "Allah sarki jeka kabata hkr kada ta damu haka Allah ya rubuti matayaya zata yi duk mai rai mamacine kowa jirantayake bnda abun Hanna bai kamata ta dingadamuwa ba tunda Allah ya bata miji tamkar uwartada ubanta." *Haisam ya ce "Iyaye daban ne da miji Ramla karmaki had'a." *Ramla tayi dariya ta ce "Miji dai irin na Hanna zaniya cewa d'aya ne da iyayenta tunda tun tanak'arama yake rainonta baya so ko k'uda ya ta6atazai iya hallaka duk wanda ya nemi ya tukara matasbd tsananin so da kulawa da yake mata." *Haisam ya mik'e tsaye daga kan kujerar da yakezaune yana dariya ya ce"Rauda ta cika gulma hakata fad'a miki?"Suka sake tuntsirewa da dariya dukkaninsu.Ramlah ta k'ara da cewa "Baka ji masu iya maganana cewa fini da gidan uban in fiki da miji ba?"Ai duk masu gata a wajen iyayena nan borori ne agidan mazajensu. Irinsu Hanna marayu su ku ma sai su ca6a da miji mai tsananin sonsu." *Haisam ya juya ya fara tafiya ya nufi k'ofar fita.Ramlah na biye da shi a baya." Ta ce "Kayi shiru saimurmushi kake baka ce komai ba." *Haisam ya ce "Aunty *Ramlah kin cika sonmagana me kike so ince miki?"Ta ce wai dana ga hira muke sai ka d'an tayani hirarkayi min musu kace Rauda k'arya take ba'ayi hakazaure ba." *Haisam ya ce "Kishi! Kishi!!"Ya motsa kumallon mata ai gara ki amayoshi yanzufa nake yabonki kin nunawa su Hidaya baki dakishi ni kuma kinzo kina son tutsiyeni." *Ramlah ta ce "A'a ba haka bane ni dai nasan kanason Hanna da yawa fiye da...................." Yasa hannuya toshe bakinta ya ce "Kema ina sonki kima dainatunanin wani abu kin ji ko."Suka tuntsure da dariya Ramla ta daga gira ta ce"Naji dad'in amsarka na gode tunda na fita daga sahun masu son maso wani." *Haisam yayi dariya ya fice, Ramlah ta rufo k'ofar tashiga cikin gida.Haisam na fitowa ya nufi 6angaren Hanna ya ta6ak'ofar yaji a datse yada hannu a aljihunsa yad'auko mukullinsa ya bud'e ya shiga ya tarar babukowa a falon sai ya nufi sama kan bene. Ya tura k'ofar ya shiga a can k'arshen gado ya hangoHanna a kwance ta takure tana rusar kuka yayisallama.yayi sallama ya shigo ta dago kai da sauri sukahada ido da haisam is ya girgiza kai t ske kifa kaiyayin da kuka mai tsanani ya rufo mata.Ya karasa gareta ya kwanta a kusa da ita. Ya jwotjikinsa kan kirjinsa ya rada mata a kunne cikinsanyayar muryace yace goge hawayenki, banaso in sake ganin hawaye a idanuwanki zamu yi watamgn.Bayan kamar minti 3 kukan da hanna takeyi yatsaya. Can haisam ya dgo da kanta suka had idosait sake kwantar da kanta a kirjinsa yana shafarlallausan gashint yace hnn meye yasa ki kuka? Karki boyemin ki fdmin gsky kuma banaso ki sakerushemin da kuka. Tayi dan murmushi cikinsanyayyiyar mury tace nayi kuka ne sbd farin cikindaya yi mun yawa da wadannan kudi masudumbin yawa da ka bamu ni da yayata.Haisam yace dalilin kukan ki na 2 kenan baki fadamin na farko ba.Ina ganin babban dalilin daya saki kuka shineAllah ya kawo miki kudi mai dumbin yawa a lkcnda babu mahaifinki wadanda zaki bawa suna sucigajiyar arzikin da Allah yayi miki. Hakane koh bahaka ba? Hanna ta gyada kai tace hakane. Haisam yace yauwa nagode baki boyemin ba.Hanna kina da ilimi, kina da tnn da hnkl matuka baikamata ki ringa damuwa akan kaddara dajarabawar da ubangiji Allah ya rubuto miki ba. Hkrda tawakalli da kikayi a bay shi zaki cigaba duklkcn da irin wnn tnn y fado miki a ri kiyi sauri ki kawar ki sawa ranki Allh ya dauke ran mahaifankiya mayr dake marainiya gaba da baya akan hakayaso ya ganki, amma sai yayi miki canji da wanimutum a matsayin mijinki kuma mai kaunar yagafarin cikin ki tamkar iyayenki.Hanna ina ganin ko 'ya'yan cikina bazan ji su araina ba kamar yadda nake kwana in yini dakekullum a zcy ta ina sake saken yadda zan farantamiki, daidi da sakon 1 banaso ki shiga matsla. Bacinranki ko kukan ki tamkar dalmar wuta ke sokamina zcy ta ki taimakeni hann ki daina saka kanki cikin damuwaDomin damuwarki tana jawo mun mummunardamuwa.Tsakaninki da mahaifanki sai addu'a nima kumanayi miki alkawrin zan dinga taya ki da yi musuaddu'a har karshen ryw ta. Ta dago. Ta dubeshi kallo mai kunshe da tsananinso da kauna tasa bakinta a gefen kumatunsatasumbaceshita rungume shi.Ranar da hanna da haisam zsu tfi da misalin karfe10 na safe ramlah dakanta take tuka musu motar takaisu filin jirgi tana dagamusu hannu har suk hau jirgi suka tadi abj. Ita kuma ta dwo gida,Haka takasance gidan shiru babu dadi sai ita kadai.washegari taje gidan su haisam ta roki hjyrsa tabata amratu tazo ta tayata zama suka taho tare .Babu abinda ramlah tasa a gaba yanzu sai shirye2yadda za'ayi ta fara gudanr da shirinta a gidanrediyo wato shirinan nata mai taken SOYAYYAGASKIYA CE. Tana ta sintiri gidan rediyo nan mai farin jini watoFREEDOM RADIO domin bincike tasan yadda za'asayar mata da filin da zata dinga gudanar dashirye2 duk sati sun karbeta da farinciki sun kumazavar mata lkcn da suka ga yadce ta dinga gudanarda shirin snn sunyi mata lkawrin zasu fara yi mata tallr shirin kafin ranar da zata fara gudanar d shirin.Rmlah bata damu da dimbin kudin da zata dingakshewa ba duk sati na sayen filin da zatayi shirinburinta shirin ya samu karbuwa a wajen jama'asakon da take so ta isar ga al'ummaa ya isa garesu.Duk rnar lahadi misalin karge 9 zuwa 10:30 ramlah zata ding gudnr d shirin snn kum duk ranr lrab dadaddare mimaita shirin. Wnn ne sati na frko daramlah zata fara gudnrta shirinta,jama'a d damasun mtso da akwatinan radiyonsu kusa dasu donkin wnn sabon shirrin da ake ta tallarsa kullumwnn gidn rediyo. Ga hirar kamar haka FREEDOM RADIO: Asslamu alaikum jama ni hjyhasana hasan safiyanu gumel zan gabatar da wnnsabon shirin tare da malama ramlah haisam shitu.Malama ramlh haisam sannu da zuwa.Ramlh: salamu alaikumHjy hassana: malama ramlah jama'a da dama sun kago suji wnn shirin sbd jin tallar shirin mai takenSOYAYYA GASKIYA CE: zamo so mu fara da jintakaitaccen tarihinki, da kuma dalilinki na kirkirownn shirin, da ma'anar kalmar SOYAYYA GASKIYACE?Ramlah: murmushi, salamu alaikum jama'a ni sunana ramlah shitu an haife shekaruna 26 nayimkrnt nursey da primary a abj daga nan na wucemkrntr gaba da pry wato secondary a kasaramerica. Bayan mun dwo nan kasa nig na shigajami'ar bayero (BUK) nayi digiri akan harka yadalabarai (mass comm). Haj. Hasana : dry ashe ma kema ta gidace 'yar jarida.Ramlah drya kwarai kuwa nima 'yar uwr kuce 'yarjarida. Donhaka nema naga ya dace nima inbadatawa gudunmawar, duk dani ba ma'aikaciar gidanrediyo bce ko talabijin nga ya kamata inyi amfanida karatuna inzo in bada tawa gudunmawar ga al'umma.kamar ydd kika tambaye ni meye ma'anarsoyayyace gaskiya ce, kuma meye dalilina nakirkiro wnn shirin? Dalilina na kirkiro wnn shirinshine sai don kawai naga 'yan uwana musulmai,hausawa, samari da yanmata yara da manya munasamun matsala wacce muke nema a wayr mana da kai akanta.Matsalar kuma itace mace macen aure da rashinsamun zaman lfy a Cikin aure.Zaki ga ko an zauna ba'a rabu ba to zman ma babudadi kagamiji da matarsa kamar ba suna son junasukayi aure ba sun zama abokan gaba kowa na kokarin ya cusgunawa dan uwansa shima ya ramalaifin da. Dayan yayi masa, babu fahimtar juna.A gsky hausawa basu yadda soyayya gsky bace.Zakiga da zrar anyi aure shikenn soyyya ta kare saizamn hkr ko zaman 'ya'ya to gsky bahaka bane.Yaune ranar farko da muka fara gudanar da shirin bazai yiwu in faiya ce muku komai ba a yanzu sai ahnkl zanyi muku bayani dalla-dalla.A yau dai bunda zan fara yin bayani akai shine,mecece soyayya? Dawa ya kamata kayi soyayya?Kuma yaya za'ayi soyayya ta dauwama har abada?Soyayya itace kaga mutum mace ko namiji kaji kana sonta ko sonsa sbd Allah, ka zauna dashi sbdAllah, kana kula da halayensa abunda yayimaikyau ka kara karfafa masa gwiwa yace gaba.Idan yayi abu mara kyau ka hana shi cikin nisihada dabaru.Kana sonsa A lkcn da yake dashi Haka kuma baza ka guje shi ba a lkcn da bashi dashi.Kana tnn a kullum yaya zaki faranta masa rai kutaimaki juna a lkcn da dayanku yake tsananinneman Taimako. Mutum ba'a gama masa halitta harsai ranar daya mutu don hka kada a gujidanuwanka don wani. Tsautsayi ya same shi hallitar ta canja.Ma'ana akwai hatsari na mota akwai wita dukmutum zi iya nakasa idan soyayyar gsky ce baza katsaneshi ba, wnn itace ma'anar soyayya.Hjy hasana: mlm ramlah munji ma'anar soyayya,saiki gaya mana dawa ya kamata kayi soyayya? Ramlah: murmushi , ko mace ko namiji ya kamataksan dawa ya kamata kayi soyayya ma'ana kasomai sonka. Soyayya takan fada kan mutumin komutuniyar da ita kuma bata ra'yin ka kunga akwaimatsala kenan.Haj hassana: wato kna nufin kenn kar ayison maso wani ko?Ramlh: yauwa zakiga wani lkc mace tanason namijishi kuma baya ra'ayinta duk da dai b'a cika samuba, nfi samun namiji nason mace amma ita batasonsa. Shi kuma zaka ga Allah yajarabeshi datsantsar sonta it kuma bata sonsa,duk wata hanya da zai bi yga ya mallakata zai yi ta bi, yayitashishshige mata yanaamaya kyautattukayake sakelullubeta kuma har abda bazai burgeta ba sbd batasonsa a zcyrta.To abu na farko daya kamata shine ya kyaleta tajeya nemi mai sonsa ita ma ta auri wanda takeso kada ya damu karya kullet bayin kanta bane dominsoyayya abace wacce Allah yake sakawa a zcyrbayinsa.Hakika bna karfafawa jama'a gwiwa akansunacewa wanda baya sonsu ina ganinhkr shinebabban magani,kaje ka auri mai sonka . Amma muddin aka takuraakayi mata dole ko akyimasadole, in namiji ne bayso, to lallai za'a samumummunar matsala bayan auran.Sbd aure yafi yin karko in namijin da macen sunason junansu.Daga karshe zanyi mgn akan yaya za'yi soyayya da dauwama har abada?bayan ramlah ta gama shirin ta a gidanrediyo hidaya ta kirata tana kuka cewar hjyr suhabib tazo tace baza ta yadda a tada wa danta hnklba irin na haisam da haka ba dole ta bar gidan.Ramlah taje ta bata shawarwarin yanda xata xaunada kishiyar ta. Bayn tfyr hanna da wata guda aka fara siyar da form din jamb ramlah ta siyar mata tayimata filling tunda tasn courses din da takesomedicine koh biochem. Kullum suna kiran ramlahda dare su sha hira sun fada mata sunje dubai,london da america xasu wuce saudia yin aikinhajj.tayi musu fatan alheri. Daga america sun wuce saudia tym din saura 2wks arfa. Kasancewarambassdon nig dake saudia abokin baban haismdon hak kawai waya yayi masa cewar gasu nanzuwa. Aka turo da mota aka dauke su. Am basumasauki a jeddah hism yace ai madina zasuwucekai tsye . Hanna ta yimurna sosai data ganta a garin rahm tayi ibada sosai. Haisam kuma yanaalura da ita sosae yanda ko mazan larabawa albarkawurin kula da matansu.haka kaya duk kantin dasukaje yana siyan mata a takaice dae yana batakulawa ta musamman. Bayan sunbar madinamakka su ka tfi inda suka suka a babban hotel dinnn wato intercontinental sbd tsadr shilarabawan ma sai wane da wane.sunyi ummurasungama suna jiran ranar da xasuje minna.ranarda za'a fita aikin hajji tun asuba mahajjata sukatashi sukayi wanka niyyyar aikin hjj suka saharaminsu da sassafe.Direbar su haisam wanda abokin baban ya basuyazo ya dauke sutunda sa sassafe don haka hannad haisam suka fito sanye da haraminsu . Ynda kefadar wahalar aikin hjji hanna bta ga wuyar ba sbdkomai nasu daban da sauran mahajjata.dominsuna tare da ambassador da iyalinsa a minna shemarsu ba a wajen data 'yan nig suke ba sunacan gaba kusa da wajenjifan shaidan taku daya 2zasuyi wjen jifan shaidan sabanin ta sauran saisunyi tfyr miles da yawa. Sunyi aikin hajji su natsecikin sauki. Snn kowa ya fara neman hanyargarinsu. Haisam da hanna sun dawo makka inda suka karyin kwana 2 a hotel dinsu snn sukajesukayi dawafin bankwana suka zuba dilar kayan amota suka nufi jedda gidan ambassador. Sunshigakasuwannin jedda kamar su babashariff dasauransu.A na gobe xasu dawo gda suka je beach indasukag larabawa da 'ya'yansu da matan su sumasuna shakawata gwanin ban sha'awa. Haisam dahanna da yaran ambassador su biyu husain dahusaina suka je shekarar su 6, husain ya jingin ajikin hnna yace anty hanna bamson ku tafi dama kuyi ta zama ana tare damu. Hanna tayi dry ta shafkansa tace husain ayihaka kuwa, muma yangidanmu suna can suna jiranmu mu dwo. Saidaiidan ka yarda in tafi da kai. Yace eh na yarda zanbiku. Su duka sukayi dry. Husaina tayikamarxatayikuka wai taj ance za'a tafi da danuwanta husain. Haisam yace lah husina kuka zakiyi? Yaceshare hawayenki wasa muke miki. Yace kin cikawayo wato ni nabar yaruwata ku kar na tafi danaku ko? Haka dae suka cigaba da shakatawacikin farinciki da walwala. Hanna ta tsai tana kallonhaisam tanajin sonshi a ranta.haisam shima ya mayar mata da irin kallon da take masa. Hanna tarike hannun shi suka mike taja hannun haisam sukfara tfy a cikin yashi lubus yayin da ruwan tekuyakeyin kukan kura ya feshin ruwan yana fesomusu.Tafiya suke a hankali suna hira Hanna ta kashemurya ta ce "Nawan, na dad'e ina mmk amma ba'ammk da ikon Allah sbd ikon Allah ya wuce hakak'iftawar ido d bud'ewa yayi yawa a wajen ubangijiya zamar da da mai kud'i talaka Ya zamar da talaka mai arziki, ya zamar d bawa sarki ya maishe da mailfy, marar lafiya ya canja k'unci izuwa farin ciki." *"Haisam ya ce haka ne, gaskiya ne."*Hanna ta nisa ta ce "Akwai lkcn dana zamana acikin k'unci da tashin hnkl, gabas da yamma, kududa arewa, sama da k'asa duk inda na waiga saibak'in ciki da tashin hankali babu wanda zan ganinaji dad'i a rayuwata, babu mai lallashina, babu mai kwantar min d hnkl. Na cire rai da k'ara samun walwala a rayuwata, nayisallma da farin ciki nayi ban kwana da soyayya,tunda wanda nake so ya ce min good bye ya tafi yabarni.Abu d'aya na rik'e shine Allah yana tare dani kumako bai yimin sakayya a duniya ba nasan zai bani a lahira musamman ranar dana zo gidankamaimakon in ganka sai akace mun ka rasu,hak'ik'a a ranar na sake tabbatarwa nayibankwana da farin ciki duniya, ko me na zama nangaba ko dawa Allah ya had'ani bani jin zan sakeson kowa a duniya." *Ba zata ba tsammani gaba d'aya Allah ya juya munrayuwata daga tsantsar bak'in ciki zuwa tsananinfarin ciki, na godewa Allah ina sake yiwa Allahgodiya fatana Allah ya had'amu a aljanna ni da kaida Aunty Ramla da mahaifina mai sona daiyayanka." *"Ta zubo da hawaye sharr! Daga idanuwanta. *Haisam ya jawota suka zauna yasa hannu yanagoge mata hawaye ya ce "Hanna kenan, gakiyarinya mai hnkln manya. *Addu'a bata fad'uwa k'asa sai dai jinkiri inaaddu'a Allah ya had'ani dake kullum dare da ranawani lkc hr in nemu yawun bakina in rasa,mak'ogarona ya bushe hawaye ya k'afe ammashuru Allah bai had'amu ba sai bayan da duk mukafitar da rai, muka cire rai akan farin cikin rayuwa sannan Allah ya had'amu.Hak'ik'a Allah yana ikonsa yana kuma yin yaddayaso a lkcn da yaga dama, Allah shine abin godiyamun gode masa." Bayan sun gama zagayen su, suka dawo wurin Husain d Husaini su ka zauna sukaci gaba da ciye-ciyensu suna hira har k'arfi 10:30na dare sannan suka nufi wajen d direba yake suka shiga suka tafi. Bayan shigar su d'akin da aka sauke su, suka yiwanka suka kwanta. Hanna ta jawo wayar daked'akin (land line) ta bugawa Ramla sukai ta hira harHaisam yayi barci ya barta suna waya suna takyalk'ala dariya yana mmkn me suke cewa a hirar.Ramla ta nunawa, Hanna ma ta na matuk'ar t farin ciki da zasu dawo gobe, Hanna ma ta nunawaRamla tana farin ciki da za su dawo gida su ganta.Har karfe biyun dare su na hira sannan suka yisallama. *Washegari da misalin k'arfin 12 na rana jirgin suHanna ya taso daga Jedda zuwa kano sun ci sa'akuwa suna isa suka iso da dilolin kayansu da sukaauno. Shehu direban ne da Amratu, Karimat amaryayaya Habib da yaya Habi su ka zo taryar su damotoci biyu su ka zo, aka shirma kayan a d'aya suka shiga d'aya suka tafi. Tun daga get suka fara ganin an lillik'a wani abumai k'yalk'yali suna shiga farfajiyar gidan suka gaan kewaye ginin gidan da k'yalk'yali an rubuta,"*COME BACK **SOON**HAISAM & HANNA. Gefe guda kuma balon-balon ce aka huhhura da yawa akayi rumfa da ita a tsakita an ajiye wanitebur dauke da wn katon ken an rubuta a jikinsa." WELL COME BACK HAISAM & HANNASunyi matukar mmkn ganin yadda jama'a suka taruashe liyafa Ramla ta hada sbd murnar dawowarsu.Kujeru aka zazzuba a farfajiyar gidan, can gefe mahaifiyar Haisam ce da Mahaifiyar Ramla dasauran tawagarsu a zazzaune. Gefe guda kuma matar maigirma gwamna ce Haj.Nusaiba Idris da babba k'awarta Rauda Shitu dasauran k'awayensu. Gefe da kuma Ramla ce da manyan k'awayentaHidaya, Aisha Sulaiman, Hauwa Mamman da wasuda yawa daga cikin k'wayenta. Mmk mararmusaltuwa zaka iya gani a fuskokin Haisam daHanna.Suna fitowa daga mota Ramla ta taso da sauri tazota rungume Haisam, ta rungume Hanna ta kamahannayensu zuwa cikin gida 6angarenta yayin da'yan wajen suka dau tafi raf-raf-raf.Daga shigar su wasu k'ayattaciyar shadda irin ta jikinta ta dauko musu dan su saka suyi anko su 3.Cikin sauri su ka fada bandakai da suke dakunansuka yi wanka su ka dauro alwala, bayan sun idarda sallah su ka cankama ado da wannankayattaciyar shaddar wadda ta sha surfani dadanyan zare. Kalar shadda ruwan zuma ce ta yiwa Ramla daHanna matukar kyau Haisam ma abun sai wanda yagani musamman ma da dora hula kalar shaddar. Ramla ta fito da su zuwa farfajiyar gidan inda jama'asuke hakika wadannan ma'aurata sun burgejama'a a jikin 'yan gulma yayi sanyi, masu tsananinkishi sun fara yayyafawa zuciyarsu ruwan sanyincewa kishiya ashe abokiyar zama ce,kala shddar ruwan zuma ce ta yiwa ramlah dahanna matukr kyau haism ma abun sai wnda yagni musmmn ma da ya dora hula kalr shddar.Ramlah ta fito dasu zuwa farfajiyar gidan inda jma'asuke , hakuka wadannan ma'aurata sun burgejama'a jikin yan gulma yayi sanyi, masu tsanani kishi sun fara yayyafawazcyr su ruwan sanyin cewrkishiya ashe abokiyar zama ce. Bangaranmahaifiyar haisam suk nufa su duka suka durkusaa gabansu suka gaisheta da kawayenta, sunaamswa cikin fra'a da farin ciki suka yi musu sannuda zuwa bayan nan sai suk dinga zagayawa wajen jama'a suna gaigaiswa. Hnna danusaiba sukarungume juna, lallai nusaiba takasance tanatsnanin kaunar hanna tun suna yara. Rudatayindama sosai akn abun data yiwa hanna ada,har yanzu takan kasa sukuni sosi duk snda sukahadu da hanna. Hanna nata kokrin janta a jikin dan ta saki jiki da itakamr yadda suke da nusaiba.Daga nan suka nufi bngaran kawayen ramlah watosu hidaya, hanna tayi mmkn yadda taga sunmikamta hannu sun gisa faram2, sukayi mususannu da zuwa. Ramlah t jsu zuwawajan kek dan su yanka. Bayannkirga dag 1 zuwa 3 hnna da hisam suna reke dawuk suka luma a cikinkek su ka yanka aka tafamusu hidamargidan ne suke fitwa dalemo kala2suna ajiyewa baki akan teburan dke gaban suwasu kuma na ajiye abinci da snacks kala2. Bayan anci ansha sai shhrrrn makadin da ka dauko y farabuga kayan kidansa wato shaba dan kwalisa yaware murya ya fr rero wakr "uwargida ran gidahaisam ya likawa ramlah da hanna kudi lkcn dasuke tsakiyar fili har mgriba ana ceshewa snnkowaccew ta far hada kayanta don kama hany gidanta.Bayn dwowrsu hanna da kwana 3 sun gamabaccin gjy sun huta sosi snn suka fara ware kayantsrba kowacce dila ka bude, snn hnna ta farawarwarewa kowtsa ksancewar hanna tasntsarabar da suka suyowakowa. Akwatiguwa akacikwa ramlah da tsaraba, tayi mmkn wnn tsarabar wanda ko ita taje abunda zata abunda zata suyowakanta kenan. Abunda ya kara bataaljaabi wataakwati daban hanna ta ciko da kayan jarirai (uniset) masumatukar kyau ta bawa ramlah tacenababyne idantahaihu. Ramlah tayi matukar gdy danuna farincikinta a fili. Waata katukar akwati aka ki gidn su hisam tsrbar hjyr haisam da babansu damratu da izziddin, suma sunyi gdy a kwarai .Ta tur direba yaa ki w yay habib d mtnsa dayaransa gaba day kowdatas suma sun gode. Batare da ramlah ta sniba hanna ta aikawa mhifinramlaha turrruka (designers) da kannan ramlah kowa da abin daya dace da shi. Sai kuma tsarabarkawayentanusaiba da raudasuma da 'ya"yan sukakaf sai da tbawa kowa tas. Kama daga masubawa folawa ruwa da masu kwasar shara gidanbabu wanda hanna bata bawa tsaraba yan uwantana nijar ne. Tana so taje tun kafin suyi tfy tayi musu sallama haisam yace sai sun dawo daga tfy, yanzuga shi sun dawo taga yana mata kame kame waibynzu ba ta bari sai ta gam jarabwar jamb tunda lkcda kusa ta zauna tayi karatu. Ramla na taya shi batahakuri akan ta baribayn is ta gama jarabawa is tatafi a nutse. Wasu littattafn karatu ramlahta suyowa hanna na karatun jamb dinda zata yi, subjects huduzata yi kwi english ,physics,biology da chemistrykuma rmlh tayi mata reegister a wata makaranta daake byr da horo na musmmn (lesson)akan jamb.Don hka hanna ta hakurada tfyr har sai bayan tazna jarabawr. Kullum karfe 4 zuw shiga haisam d kns yake ki hanna makarntr da take lesson ya jrt tagama ya dawo da ita.Hanna ta kasance tana karatu haikan domin harta fara manta karatun da sukayi a sakndiri ammayanxu katatun da ta keyishiya ke tunomata dakaratunta na baya.lkcn daza ta jarabawa ya ragekwana3 haisam yaje jamb ofisya karbomata centerta. A management za tayi danhaka ranar litinin da safebakwai na safe acan tayi mata. Haisam ya kwo takafin ta fito daga motar ya sumbaci kumatunta yayimata fatan alheri Allah ya bada sa'ar jarabawa dagakarshe yace mata da zarar ta gama ta kira shi awaya yazo ya duketa. Hanna na shigdakin jarabawa aka mikomatakustion paper da ansa sheet sai kawai tayimurmushi data karanta tambayoyin kamar cintuwo yafi su wahala gurinta. Nan da nan hanna taciccike ta gama, ta zauna kamar minti 30 bayan tagama tana zaune kawai tana kallon masuhada zufa da cizon biro da kallonsillin taji tausayin wasu danbabu yadda za tayi ta taimake su ta basu amsa.Taso ace wani ya rigata mikewa amma har ta gajida zama babu wanda ya gama har yanzu, sai tamiketaje ta kaiwa masu tsaransu sunyi mmk dasuka ga har ta gama 1 daga cikin mlmn yaceta sake zama dai ta duba ko tayi mantuwa hanna tce babukomai ta gama. Tana fitowa dagadakin jarabawarsai ta nufihanyrgetdin fita daidaikantin wata biyerabiya tagabenci, bayan ta gaishe da matar cikinfara'a taroketa zata zauna ta jira maigidant zaizoyadauketa. Bayan ta zauna ta bude jakarta ta zarowayarta, bugu1 taji haisam yadauka shimayayi mmk da yaji tace yazoya dauketa ta gama.Yace gashinan zuwa yanzu-yanzun nan,daya daga cikin mlmn da suke tsaransu a dakinjarabawa ta hango ya nufo inda take, yanakarasowa yayi musu sallama suka amsa sai yayiwahanna wani lallausam murmushi yace minti2 danAllah yan mata zamuyi mgn.Cikin mmk hanna ta tambaya tace ni? Ya gyada kai yaceeh ke,Danke n fito.hanna ta harareshitace mlmyi hkrbazan iya zuwaba saboda kana mgn da matar aureyanzun ma haka ina jiran mijina zizo ya dauke ni.Kamar ta dabawa mutumin wuka a kirji, haka yazabura ya rike kirji yana fadin subhanaAllah yanzu ke matar aure ce, ynzun kina nufin kina da aure?Karki boye min fadamin gsky. Hanna ta sake gyaramayafinta tacebabu zancen wasa tsakanina da kimalm ban sanka, baka sanni ba yaya za'ayi in yimaka wasa?ya rike baki yana sosa keyadadayahannun fadi yake subhanaAllah yanzu ke matar aurece, yaya za'ayikenn? Ni gsky na ganikuma inaso zan iy fadawa cikinwani hali dan wlh aryw ta ban taba ganin yrnyr da nakamu da sontabaa 'yan mintina.Cikinfushi hanna tamike ta kalli matar nan mai kntitace madam sai anjima xan bar wajan nan. Matar na cewa ah ba yanzu kika yiwa maigidanki waya bayazo ya daukeki, ya z'ayiki tafi? Hanna bata iyajuyowa ta bata amsa ba sbd kallon da mutuminyake yi mata yayi yawa. Ta kada kai ta nufi get dinfita ba tare da san inda zata ba.Tanafitowa ta tsaya cak ta kalli gabas da yamma sai tahango wata 'yar yrny wacce shekarunta basuwuce goma ba tana tsugunne a jikin katangagafaranti da kwanika akaida alama dai mai tallarabinci ne.Yrnyr kuka take haikan cikin sauri hannata nufiinda yrnyr take tan karasawa wajen yrnyr babuabinda ta faragani a jikin yrny sai shatinbulalahar wani wajen zaka iya hango jan jininfatarta ta fashe. Hanna ta ggce ta tsugunna a gabanyrnyr kafin ta tambayetme yasameta tafara zubarda hawaye.tasa hannu a jakarta ta zaro wani hankici fari maikamshi ta mika wa yrnyr tace goge hawayenki.Yrnyrta karba tana gogewa kafin ta goge hawyenda ya zubo wani ya sake tsiyayowa.hanna ta gogenata hawyen tace da yrnyr yaya sunan ki ? Cikinshashekar kuka yrnyr tace sunana abida abida daina kuka goge hawayenki ki fadamin dalla2 abinda ya sa kike kuka zan taimake ki in Allah ya yarda.Hanna ta tambayi abida.Abida tace tallr wake da shinkafa nakeyi sai wanimutum ya kirani shagonsa yace in kawo masa zaisiya na ajiye farantin abincin a kofar shagonsa, sai yce in shigo cikinace ai kofar karama ce farantinbazai iya wucewa ba sai yace to in dauko masakwano 1 in kawo masa.Na dauko kwanon abincin na shiga shagon saiyace mun zai saye abincin duka zai biya ni harmaya kara min kudin fiye da kudin abincina amma sai na yadda ya kwanta dani, nace na ki niba 'yariskabacesai kawaiya rufe kofar yakama ni da krfi nakwalla ihu dakarfi shine ya dokeminbakina har yafashe ya bude min kofar yasa kafa ya maujeni nafado waje kan farantin abincin ya zube shine najegida na fadawa babarmu shine ta zaneni da bulala ta koroni tace duk inda zan nemo mata kudinabincinta inje in nemo.Yanxu bansan yadda xanyi ba. Abida ta rushedakuka mai tsanani.Hawaye fal a idon hanna tayi shiru can tace abidababarki ita ta haifeki ko kuma kishiyar babarki ce? Abida tce uwata ta mutu ubana ya mutu wnn yayarmahaifiya ta ce take rikeni.Hanna tace bata da 'ya'ya sai ke kadai? Abida tacetana da 'ya'ya 'yar autarta ce ma sa'a taHanna tacesu basa zuwa tallar saike? Avida tcebasa zuwa sunagida kullum wata rana kumasu tafi makaranta. Hanna tace kefa bakya makarantar? Tace an cire nida dai ina zuwa ajina ma 3 yanzu na daina zuwa.Hanna ta jawo abida jikinta ta rungumeta ta fasheda kuka mai tsanani, tausayinta ya kamata ta tunorayuwarta irin ta Abida ada maraici bashi da dad'i.Can ta d'ago da kan Abida ta goge mata hawayenfuskarta ta ce"Abida d'auko farantinki zo muje kan tudun can mu zauna. Hanna na gaba Abida dauke da farantin abinxutana biye da ita. Ihum da Abida ta tsala ta kifar dafarantin dake kanta shine ya razana Hanna tajigabanta ya yanke ya fadi ta juyo da sauri. Sai tagawata mata dauke da bulala ta cakume rigar Abidata baya tana kokarin taftaf ka mata murtikekiyar bulalar dake hannunta. Hanna ta taho da sauri tafisge Abida daga hannu matar.Yayin da Abida ta taho a guje bayan Hanna ta la6efadi take "Hajiya ki taimake ni karki bari ta dakeni.Matar fada take harda kumfar baki danna ashartake tana cewa "Kyaleni da tsinanniyar yarinyar nan yau saina kusa kasheta idan ma bn kasheta ba,ta sani a uku abincin naira na dukan naira har darihudu da hamsin ta zubar min."Hanna hkr take bawa matar kamar zata durkusamata amma matar nan fadi take yau ta shiga ukuasara ta sameta sai ta daki kudinta. Sai da taga magiyar da Hanna keyi tayi yawa.har da hawaye ne yakezubowa daga idanunta sannan matar ta tsagaigatata fara sauraron abinda Hanna ke cewa. Hanna tagoge hawayen fskrt ta ce d matar "Kina musulmabahaushiya 'yar uwata ina rokakrki ina hadaki da ubangikinki ya bazaki saurareni ba?" Haba baiwar Allah wacece hasara ce ta samekihaka har zaka manat da k'alu innalillahi wa'inailaihin raju'un duk sanda masifa ta same shi. Kina tadankara ashar kina fadin kin shiga uku kin lalacesbd Allah ya dora miki asara, ke kuwa baiwar Allahbaza ki tattara al'amuranki gaba daya ba ki mika wajen mahaliccinki mai bayarwa mai hanawa ba?" Matar ta tsuke fuska yayin da haushin Hanna yarufeta ta ce "Malama wa'azi kike mun ko kuma jajekike mun?" Don na kasa gane abinda kike nufi. Kinganani in daki 'yata kuma kina tsuyani akan nayimasifa dame zanji da asarar da nayi ko kuma dafadan da kike min?" Hanna ta nisa ta ce "Yi hkr ba fada nake yi miki bashawara bake baki a matsayinki na 'yar uwatamuasulma ki rike kalmar K'alu innalillahi wa'innaialaihir raji'un a lkcn da masifa ta afka miki zaki gayadda Allah zai saka miki da alherinsa." Matar ta ce "Wannan kuma tasha nawa nake fada."Hanna ta ce "Karki ki shawarata nasan kina cikin6acin rai da damuwa amma kice 'Kalu innalillahiwa'inna ilaihinr raji'un." zaki ji sanyi a ranki." *Matar ta ce "Bazan ki ta ki ba yarinya innalillahi wainna ilaihin raji'un." *Hanna tayi murmushi ta ce "Yauwa sai ki jira Allahkiga sakayyar da zaiyi miki."Ta ce da Abida ta tsince kwanikan da suka watse akasa suzo su karsa wani dan dakalin siminti suzauna.Suna isa wajen suka zazzauna Abida kuma tatsugunna a kasa cike da fargaba.Hanna tasa hannu cikin jakarta ta zaro kudi nairadubu dubu guda goma ta mikawa matar, matar tabude baki tana jujjuya kudin."Hanna ta ce "Naki ne wannan ki kara jari. Am,a dn Allah ki canja sana'aki daina dorawa Abida talla ki bar Abida ta komamkrnt tayi krt ta daina talla." Ta zaro wata dubu goma ta mikawa matar ta ce"Wannan na Abida ne ki saya mata uniform datakalmin mkrnt da littafai da jaka ta koma mkrnt.." Sai matar ta rushe da kuka ta durkusa a gabanHanna tana godiya.Hanna ta kama hannu matar ta zaunar da ita ta ce"Babu komai Abida kanwa ta ce daga yau zandinga taimakonku insha Allah." Hanna tasa matartayi mata tayi mata kwatancen gidansu sannan Hanna ta rubuta lmbr wayarta a wata 'yar takardata mikawa matar ta ce idan suna da wata matsala tabuga mata waya ko nawa ne zata taimaka musu itadai fatanta a daina dorawa Abida talla a dainatsangwamarta don Allah. Hanna ta dora da bawa matar lbrnta tana nunamata tasan irin halin da Abida take ciki kumagallazawa maraya haramun ne. Matar tayi nadamatayi dana sani taji kunyar Hanna sosai. Kuka takekawai tana nemangafara wajen Abida ta yafe mata." Haisam ne ya karkato da motarsa zai shiga get dinmkrnt ga mmkns sai ya hango Hanna zaune a gefeita wasu. Ya karkata motar ya nufi inda suke cukinrikicewa ya fito daga motar ya nufi inda suke sbdya hango su suna mgn suna koke-koke. Ba tare dasun ga zuwansa ba sai suka ga mu2m a kansu ya tsaya kawai yana kallonsu cike da mmk. Hanna tayi sauri ta goge hawayen dake idonta tayimurmushi dole ta ce "Yaya yaushe ka zo, yayaakayi kasan ina nan?"Ya ce "Zan shiga ciki na hango ku anan, lafiyawadannan fa, kukan me kuke yi?"Matar ta rushe da kuka tana cewa tsakanina dakusai gdy Allah ya saka d alheri."Hawaye ne yakezubowa dg idn Hanna.Haisam ya zaro hankici a aljinhunsa yana gogemata yaja hannunta suka shiga mota Abida d babarta suna ta dagawa Hanna hannu suma sunata kuka, Haisam yaja moyar suka tafi." Yayi shiru bai cekomai ba can ya nisa ya ce "Wannan yarinyarmarainiya ce ko?" Hanna ta kalleshi cikin mmk ta ce"Yaya akayi ka sani." Haisam yayi murmushi ya ce haba 'yar babanasanki nasan halinki fiye da kowa ina ganinbabbar matsalarki yanzu a rayuwarki bata wucemahaifinki wanda ko yaushe ina miki nasiha kiyihkr ki cirewa ranki tunanin mamaci duk wanda yamutu ya mutu kenan bazai dawo ba har abada, naga yanzu kukan naki ya wuce maraici da kikeciki ya koma kan duk marayun dny kuka kikemusu, kamar mu zuga ki nake nace bana son ingakina kuka hankalina yana bala'in tashi kinki ji." Hanna ta marairace ido yayin da taci gaba da zuboda hawaye Haisam yasa hannu daya ya jawotajikinsa yana tuki da dayan ya ce "'Yi hkr to fadamunyadda kika hadu da wadancan mutanen." Hanna ta gyara zama ta goge hawayen idonta tafara bawa Haisam lbrn abinda ya faru."Dai-dai lkcn sun iso unguwarsu Tarauni ya karkataya shiga wajen da ake sayar da kayan ciye-ciyenmakulashi wato Oasis. Hanna ta ce " zaka ci kek ne?"Da ka bari naje gida sai inyi maka."Haisam ya ce hana ai sai whlr tayi miki yawa tunshekaran jiya rabon da kiyi barcin krki musammanjiya kusan a zaune kika kwana kina krt.Tea din ma dana hada miki da safe ko kr6a dayabaki yi ba kika barshi kuma yanzun na tabbatabaki ci komai ba, naga duk kinyi wuri-wuri shinenake so in saya miki wani abu anan."Ya tsaya a bakin wajen ya ce da ita su shiga ciki, suka fito suka shiga. Hanna ta zazza6i abinda takeso kamar meat pie da kek da shawarma sai juicesna gwangwani da yogot. Bayan Haisam ya biya kudin suka zazzuba musu aleda. Sun fitowa bakin wajen Haisam ya kira almajiran dasu ke bara a wajen ya mika musu ledojin duka yace su je su rarraba su ci." Hanna tayi kasa tana kallon ikon Allah, Haisam yakalleta yayi murmushi ya ce kina mmk ne?"Yanzu na canja shawara baza ma ki ci kayan zakinnan ba gara mu wuce Tahir Guest place ki huta saida yamma ko ma da daddare mu koma gida,Hanna tace amma ai ya kamata mu koma giidaanty ramlah tasan na dawo. Haism yace zo mu tafike kinfi jin tausayin anty ramlah akan ni komukicenty ramlah xanje na gani. Sun isa kayattacenkatafaren hotel din tahir guest place dake lmidocresent. Kayataccen daku suka kma dai dauke da falo da dinningarea, ga daki mai dauke d katafarengado da bayi a ciki. Abinci kala2 ma'aikata sukeshigo dashi suna jerawa akan dinning table,hannada angon ta sunci sun sha sun gyatse sun rage.Haaisam ya riko hannunta suka nuf cikin daki.kaitsaye bandak suka shiga dan suka shiga dan su watsa ruwa suji sanyi a jikinsu duk da sanyin splitAc daya gauraye dakin daga can suka dauroalwala sukazo sukayi sallar azahar, bayan sun idrne suka kwanta akan katafaran gadon nan, yayinda hannataji gabadaya kashin bayanta ya hau karsbd gjyr da tayi sbd tsabar zama ga barci a idonta .Haisam yana mata tausa har barci mai dadi yafar surarta . Kamar a mafarki taji haisam na cewagsky nusaiba kawarki na sanki yanzu nan dagaofis din mi girma gamna nake,na karbomikitakardun kwangila nusaiba tasa a baki ta miliyan25 baifi kikashe miliyn 10 ba wajen gyaran jiki zaki gina da saloon da wajan kunshi. Rauda ma tamiliyan 25 aaka bat zata zuba kaya aa sabon gidnda ta ginawa wan babanta (interiordecoraton),bayan kwaangilar titi da suka banikwanakin baya tamiliyan 200, yanzu ma sun sakebanikwangilar ginaa wani titin shima wasu miliyoyin ne gashi su biyaaakan lkcina gamawa.Hanna tayi zumbur ta tashi zaune tna sauraronsa,yacigba da cewa na saya miki wnn katon filin najikin katangar gidana anan za'a gina miki masallacida mkrtr islamiyya da ki kace kina sona gina miki.Hanna tace inason a gina gidaje 2 a gefe dan inaso in daukoiya salma da uwarbiyu su zauna a 1, wadakuma ya zauna a 1 yana kula da supermarket.Haisam yace filin babbane ai zai isa. Hanna tarungume haisam dan murna ta sumbaci bakinsa,tace thank u my dear shima yarungume ta daganan suka shiga farantawa juna. Bayan kwana 2 da sassafe hanna ta tashi ta fara shirya kayan tfy aakwati gudakayanta dana haisam sai akwatintsaraba da zata kai musu guda 3. Ta leko tawindota kira shehu direba y lubga a cikin but dinmotar da zasu tafi da ita kirar CRV. Wayar hanna cetatashi ramlah da haisam daga barci ramlah ta lalubi wayar ta dauka hanna tace yayata yi hkr najimuryarki kamar kinabarci na tasheki gshi ba'a sontashin mai ciki daga barci wlh banji dadi ba yi hkr.Ramlah tayimurmushi tace lah kanwata babukomai wlh kin tashi lfy? Hanna tace lfy kalau damansllama zanyi miki sbd kar inzo in buga miki kofa dasassafe, saidai ince sai Allah ya dawo da mu.Ramlah tace haka. Tsaitsaye saurikike hour baza kibari a gama break fast ba kuci. Yallabi ne azazzale ki yce ki shirya da sassafe zaku tafi ko? To ai kuwaga shinan yana t shirgar barcinsake ya hanaki kiyibarcinki. Haisam yayi zumbur ya mike y fadabandaki da sauri, ramlah tayi dry tace yanzun nankingn shi yajimunamgnr ya mike ya fada wanka.Hanna tayi dry tace cemin yayi in tashi da asuba in shirya tfyr sassafe zamuyi, dan da subama ya dingwaya na duka ma ya shirya, to shikenan bari in jirashi. Ramlah tce ki fitokizo bangarensa ki samemumuci abinci, bari in yiw su zuwira waya abangarena inga sun gam abinci su shigo manadshi, hanna tace to gani nan zuwa. Suka ajiye waya. Suna cin abinci sunahira hanna ta dubi ramlah tayimurmushitace antynah ina ganin kin kusan hihuwaba da sai nayi wataguda acan amma yanzu sati 1zanyi kawai. Haisam ya harari hanna yace waike mewayo kinaso dai kice min komin abuna duk darakiyar da zanyi dan karki dde kina so kice min sai kinyi sati acan, kinsan di bazan iya mikewa a garinsurukai in ta kwana har sati guda daya ba. Hnna tamarairaice ido tace n dauka saukeni zkuyi ku juyuidan na gama kwanakin ku dauko ni, hisam yace inkin dauka ma to ki suke ai kafarki kafata kwana 1jal zamuyi. Ramlah tace a'a bai kamata ba ai dole tayi dan kwanaki yallabai.haisam ya lura da hannata kule tana daf da ta fashe da kuka sai ya haulallashinta yana cewa to shikenan aI amarya batalaifi za muyi shawara a hanya dai.Ramla tace da hanna ga atamfofi can a jakanasa shehu ya dauka ya saka a mota da kudi aambulan ki rabwa 'yan kungyata, hanna tace kaianty ramlah har yanzu dai wahala baza ta kare ba?Ramlah tace babu ikon tashi dga nan naje nijr nabude kungiya Allah shine yake bani abundanake taimakonsu hanna tayi gdy dga karshe sukdinguma wjen mota, haisam na cewa ramlah lailla2ta dinga kwana da wata a daki ta daina kwanciyaita kadai ko nakuda kan iya tashi cikin dare, yashaida mata baza su dade ba zasu dawo. A gidanbaya haisam da hanna suka kame direba na jansu suka tafi. Sun kamahanyar garin Dashi cikinjanhuyar niger, tfy suke kamar ba a mota suke basanyin Ac na tashi yayin da sautin kida na tashi ahnkl. Hnna ta kwanto akan cinyar haism cikinshagwab tace yaya nifa so nake inyi sati guda aDashi sai mu wuce babban mutum inga iya salmi daga can sai mu shiga kazaure wajen uwar 2 dukmuga lfyr su. Haisam yace amma sati 1 yayi yawakiyi kwana 4 dai ni zan wuce mradi gurin aboknain kin gama kwanakin sai muzo mu dauke ki mutafi babban mutum da kazaure a ranar sai mu wuceabj zanje inga yadda suka sayr mun da motoci snn sai mu huta a nicon da sharaton, bayan kwana 4saimu koma kano. Yayi miki ko baiyi ba? Taceyayimin tunda yayi maka nawan. Sun isa garinDashi yayin da mmk da farinciki ya lullube danginhanna. Hanna da hijir suka rungume juna sunamurna.kawu ahmd yasa aka shimfidawa haisam tabarma a zaure suka zazzauna dangi na tashigowa suna yi masu sannu da zuwa.Nanfa aka garzaya kasuwa dan siyo kayanabinci iri iri wanda xa'a dafawa wadannanhadaddun yan gayun baki.fura mai dadi dakirdirmon nono mai kyau aka kawo musu kafin agama abinci. Haisam yasha fura da nono sosaikasancewar yanason fura da nono. Bayan sunyi sallar azahar daidai lkcn abinci ya nuna sai aka farazuwa a jerawa haisam nasa. Direba ma aka kaimasa nasa inda akayi masa shimfida. Hanna nacikin gida tana cin nata kawaye da dangi duk sunzagaye ta kai kace biki akeyi a gidan. Haisam dakawu ahmad suna cin abinci suna hira sai gdy kawu ahmad yake yiwa haisam. Bayan sun gama cila'asar tayi sukayi sallah saihaisam ya shaidawakawo ahmad cewa zai wuce maradi sai nan dakwana 4 xai dawo ya dauki hanna. Kawo ahmadya roki haisam ya kwana mana kafin ya tafi. Haisamyace bakomai ai dare baiyi ba zasu tafi kawai. Yasa yarasuka dinga jido akwati suna shigarwa cikingidan, yace su cewa hanna ta fito suyi sallama xaitafi. Hanna ta bude akwatin kayansu tacire nata tabar mai nashi acikin akwatin tasa aka kai mai mota.Tasa hijab ta fito ta iske haisam a zaune a zaure shikadai.ta durkusa ta gaishe shi ya amsa cikin fara'a yace kinga abinda nake gudu ya faru dani? Hannatace yaya, meye faru da kai? Yace daidai da rana 1banason in rabu dake amma gashi kin jawomin sainayi kwana 4 xan ganki . Hanna tace Allah sarkikarka damu GANGAR JIKINA ne kawai bata tare kaiRUHINA yana tare da kai ai. Su duk sukayi dry.haisam yace aini yanzu daga GANGAR JIKIN harruhin so nake su zamana tare dani, koda yakebabu komai tunda mu duka muna kasar nijarturirin numfashin ki zai dinga buso ni,Hanna tayi dry tace nima xanyi missing dinka.Haisam ya mike tsaye yace babu wani, dadin bakine kin samu hijir kuna hira yaushe xaki tuna dahaisam. Hanna tace ai kuwa da kasan irin hirar damuke da hijir dakace mu shekara muna hirardomin asalin shakuwr mu hirar ka take tayani. Haisam yayi murmushi ya mike yace har na fara jinkasala xan tafi ni kadai in bar abinda nafiso a rywta. Yanxun dai abin da nakeso dake ki samu biroda takarda ki rubuta duk wadanda kikeso a dangia taimakawa da jari ko kuma wata bukartar su dasuke neman taimako kiyimin total xan canjo kudin nijar a can. Idan nazo sai na baki ki rarrabamusu.hanna ta amsa masa da to gami da gdy danuna farin cikinta a fili. Tace kuma inaso a ginawakungiyar anty ramlah office wanda zai zama ananza'a ringa taro kuma duk wani mai sha'awartaimakon su xa'a iya kaiwa can.haisam yace this is a ver good idea sai kicewa kawo ahmad ya nemofili ya kiyasta nawa xa'a kashe wajen ginan sai abar masa ya gina. Hanna ta rakashi har cikin motasuka ringa hira kamar bazai tafi ba shidai sakenanatawa yake baiji dadi ba zaiyi kwana 4 baiganta ba.ita kuma hkr take bashi har ta lallashe shi ya tafi snn ta shigo cikin gida.A kwanaki4 dahanna tayi ta ziyarci yanuwa daabokan arziki da ywa a cikin garin dana wajengarin kowacce tana kawo kukanta wasu talauci yaishe su sun rasa yadda zasu yi, wasu kuma auren'ya'yansu ya tashi basu da kudin siyan kayandaki.hanna ta kaiwa 'yan kungiyarta ziyara bayan shela da akayi aka tara su inda suke taruwa. Sunyimurna dawadannan atamfofi da kudade da hannata raba musutace inji ramlah tace a basu, tashaidamusu wnn kadan ne kafin ta tafi zata sake tara suta raba musu. Kudi fiye da wadannan daga karshetayi musu albishir da cewa xa'a gina musu ofis da hall za'a zuba kujeru wurin da xa'a ringa meeting.Ta kara da cewa da yardan Allah kungiyar xatabunkasa xa'a ringa turo tallafi koh da yaushe.Murna wacce baza ta misaltu ba a wurin 'yankungiyar sai gdy da shi albarka sukeyiwa hanna.Da addu'ar fatan alheri a rywr ta. Ranar da hanna ta cika kwana 4 a garin tasan daga inda gari ya wayehaisam zai dira a garin gashi bata gama ziyararyanuwa ba don haka karfe 7 a gidan inna hauleyayi mata. Tana shiga tayi sallama ta iske inna hauleda indo suna sana'ar da suka saba.inna haule tasaindo a gaba tana fada indo na tikar aiki. Inna haule ta daga kai taga mai sallama sai taga hanna tadukar da kanta kasa ta kasa hada ido da ita sai tamike sumsum ta shige dakinta. Indo ta tawo dasauri ta rungume hanna ta rushe da kuka. Hannatazubo da hawayen idonta tace indo wajenki nazona dauka zan ganki a wajen taro ban ganki ba na tambaya akacemin kina gida baki zo ba ammanabada kasonki an kuwa baki? Indo tace anbanikinsan bani da halin fita inje wajen taro sbd aiki.Hanna tace bari na shiga mu gaisa da inna sai nazomu shiga daki muyi mgn.hanna tayi sallama dakin inna haule snn tashiga ta durkusa ta gaishe da ita ga mmkn ta saitaga hawaye fal a idon inna haule ta zauna taceinna lfy kike kuka? Haule ta sake rushewa dakuka tana cewa ganin kisai bello ya fado min a rai, tsananin bakin ciki da takurawar dana haddasa masa a snadiyyar gallazamiki danayi.Bello yayi min biyayya, ranar da zai rsumin rabudashi yana kuka yan rokona in sassauta miki AllahAkbar sai gawarsa aka kawo min ya mutu da bakincikina a ransa, duk dani uwrs ce mai zan cewa Allah amma Bello mai biyayya ne nasan zai yafemin.Hanna ki yafe min a madadin Bello da ke kankiabinda nayi miki.Allah kenan ya canja miki rywr ki kin min fintinkau.Yanzu kira kawun ki azo a raba gadon bello a bakinaki. Hanna ta zubo da hawayen idonta tace inna na yafemiki daman ba bello kika yiwa ba nikika yiw shi daiyn damuwa a ransa duk sanda zaiga kin gallazamin.Snn zancen a rabagado, inna ki rike duka na yafemiki ina ganin yanzu gadon babuabind zaiyi min ma'ana baki bani kasona ba a lkcn da nkebukatarsa.A yanzu haka idan na karva sai dai na bayr sbdbabu abinda na nema na rasa kinga da in karba inrabaki da shi in bawa wani gara ki rike duka tundaga tsufa ya karu karfi ya kare. Mai taimakonki ya rasu,Ni ya kamata na baki ba na kar6i naki ba. Ni aganina da kin koma sbn gidan can na siminti ki barna kasar nan Inna ki huta sbd kar gidan ya zamaasara shi bai zauna ba ke baki zauna ba, Allah yajikan Bello." Inna Haule ta ce "Amin Hanna na gode." Can zuwa wani dan lkc babu wanda yayi maganasai Hanna ta nisa ta ce "Inna shawara daya zanbaki, mai zai hana ki bar Indo ta huta da wannanaiki da zagi da takw sha shekara da shekaru innaduba kiga yadda Indo take tamkar baiwa ita da'ya'yanta ita ce gona, ita ce surfa da nika. Inna indo baza iya tafiya ta barku ba, ina zata kai 'ya'ya nan?" A nan dai a jikinki take samun dan abun da zata cida yayanta ku zauna lfu mana amma aikin yayiyawa." Inna Haule ta nisa ta ce"Hanna naji abundakika cemun ni yanzu jikina yayi sanyi in Allah yayarda zamu koma sbn gidan Bello mu zauna har daindo da 'ya'yanta ko ni kaina nasan bani da wata 'yar uwa mai taimakona me min hidimomi kamarindo, yanzy kwanaki amai da gudawa nayi cikin dareIndo ce a kaina har gari ya waye ita ta wankekayan kashin d amai.Gaskiya kike fada mun kirawo Indon itama in nemigafarar ta." Inna Haule ta rushe da kuka."Hanna ta kwallawa Indo kira ta taho da sauritaxota durkusa ta ce "Gani."Hanna ga gyara zama ta yiwa Indo bayani Inna tasaduda tasan bata kyautawa don haka ta dainatakura mata. Amma sai bayanin Hanna ya bambanta da tunanin Inna Haule Hanna ta ce "Indona taho miki da kudi isasshe kawuna zai tsaya mikia rushe 6angaranki a gina miki na siminti kema kizauna da 'ya'yanki za fasa miki kofar shigarkudaban. Zan baki jari mai yawa zan baki din sana'a kina cinabinci da 'ya'yanki, na dauki nauyin krtnsu sukoma mkrnt, kema ki huta da wahala a rayuwarki.Indo ta rushe da kuka tana gdy, Inna Haule nakuka itama tana neman gafarsu tana cewa "Ai bazaayi haka ba idan Indo ta barni dawa zan zauna ya dinga taimakona, ga tsufa bana iya yin komai dakaina tunda ba gani nake sosai ba. 'Ya'yan Indo sune aikin gonata sune suke mun tallajikokina na cikina ko aikensu nayi basa zuwa.Hanna idan kika yi haka kin raba zumunci." Mu dai kaura can gidan siminti da Indon muzauna." Hanna ta ce "A'a Inna ai ba'a sabo dawuya, ya yan Indo krt zasu yi ba talla ba."Indo ta ce"A dangi zaki nemi wata ku zauna ni kam ai nayigaba shekara nawa ana azabtar dani da 'ya'yan angutar dani sai in ki ba dai ni ba nemo wata." Hanna ta ce "Indo ma 'yar aiki zan daukar mata itata kwanta ta huta."Inna Haule ta rike baki tana maimaitawa 'yar aiki?Indo da 'yar aiki.."Yaro ne ya shigo ya ce "Wai Hanna tazo anzodaukarta inji wani mu2m a cikin mota."Hanna ta cemusu tana zuwa ta fito sai taha Haisam ne ta karsacikin motar bayan ta gaisheshi ta shaida masacewar gidan su Bello Madu tazo zata gaishe da mahaifiyarsa. Haisama ya harareta ya ce "Gidan tsohon mijinki kika zo ga alamar kuka nan kinyi wato kun tunabaya." Hanna ta tuntsire da dariya ta ce "Kai Yayawanda ya mutu ma kishi kake dashi?"Ba wani tuna baya da akayi ta ganni dai sai ta haukuka." Hanna ta tambayeshi kudi tana so ta raba musu."Wata 'yar akwati ya nuna mata a kujeran baya tanabudewa sai taha kudi himili guda ya ce ta dibiyadda zai isheta." Ta dibi kamar dubu dari dahamsin idan aka canja da kudin Nigeria, ta ce yazosu shiga ya gaishesu. Bayan sun shiga Haisam ya zauna kan watatabarma a dakin Inna Haule suka gaisa sai Hanna taajiyewa Inna Haule dubu hamsin ta ce gashi ta sayigoro. Ta wuce dakin Indo ta samu Indo nata rusarkuka, ta zauna tana lallashinta ta mika mata dubudari ta ce ta fara yin jari sanna ta tabbata yayanta sun ci gaba da mkrnt. Ta kuma ce mata duk sanda take da matsala taje dafadawa Hajir ko kawunta Ahmed zasu fada mata awaya zata aiko da mata ko nawa ne, kuma karshewatan nan zata da torowa kawunta kudi a fara yimata gini. Indo tayi farin ciki tayi murna matuka. Ta shaidawaHanna cewa yau jinta take kamar a aljanna sbd lkcnguda an 'yanta ta fita daga sahun bayi. Sukadunguma suka fito harda Inna Hauke suka rako suhar bakin mota suna koke-koe suna godiya,Haisam yaja suka yi gaba,A zauren kawu Ahmed aka zazzage akwayin kudiana kasafi ga sunan kowa a jikn takarda da yawantallafin kudin da za'a bashi.." 'yan mata goma shabiyu Hanna ta yiwa kayan daki wasu jari ta basu,duk an mikawa kawu Ahmed ya raba musu. KudinNigeria miliyan biyu Hanna ta bawa kawunta cheek, matarsa duba dari biyu da hamsin suyi jarisu gina sabon gida na suminti, kawu Ahmed yajikamar a mafarki yayin da kuka ya 6arke masa yayigodiya sosai." Haka Hajir ma tasha gdy da kukanfarin ciki." Haka dai Hanna ta zuba kayanta a mota suka shigadireba Shehu shima ya shiga ta tashi mota 'yan uwacunkus a bakin motar ana daga musu hannu sukatafi, farin ciki fal a zuciyar Hanna harma kamar tafisu farin ciki sbd taimakawa danginta data yi sun fitadaga tsantar fatara da rashin da suke ciki. Sun nufi hanyar Babban mutum a janhuriyyarNigeria.K'arfe uku dai dai a kofar gidan iya Salmai tayimusu. Hanna ta shiga gidan da sauri yayin da takekwada sallma waige-waige take taga ta ina iyaSalmai zata fito tayi tsalle ta rumgumeta." Wada tagani a bakin kofar dakin a tsaye yana da damuwa."Hanna ta karasa gareshi cikin sanyin jikida dimuwa ta ce "Wada lafiya, ina iya Salmaintake?" Wada karka ce min iya ta rasu." "Yayin da ta fara hawaye." Wada ya ce "Bata rasuba gata nan a zaune a daki tana kuka tun jiya dayamma taki ci taki sha." Hanna ta fada cikin dakinda sauri ta iske iya Salmai tayi tagumi tana kukatana ganin Hanna sai ta sake tsala kuka. Hanna ta c"iya lafiya meya faru?" Wafa ya shigo ya zauba ya ce "Bansan takamaimaimeke damunta ba jiya da rana ita wani mu2m sukaje wani gari ni dai bata fadamun sunan garin dasuka je ba sai na ganta ta dawo da yamma Zaharaddeen Shomar Whatspp 08168575100 GANGARJIKINSA NA AURA 3 Part 4 Posted by ANaM Dorayi on 06:27 PM, 30-Apr-15 Under: Gangarjikinsa ta Aura Tana kuka tace min wai yau ido da ido taga mallamhabu mahaifinki har sunyi mgn dashi. Hanna tazabura ta daka tsalle da dafa kirji ta fara ja dabayata fita ta daga dakin taje tsakar gida ta zauna yayinjiriyake daukar ta bata gani sosai, gabnta ya hau faduwa ta tabbata lallai ciwon so ya zautar da iyasalmai har mlm habu ya fara. Yi mata gizau. Haisam ne ya shigo ya tarar da hanna a tsugunneyaje ya tabata yaga tafi dagowa yasa hannu tatasheta tsaye yaga kuka takeyi jikinta gaba1karkarwa yake idonta yaki budewa gaba 1.Ya girgizata ya kiran sunan ta, ta rushe da kuka tarungume shi tace yaya dama ana mutuwa a dawo? Yace ban gane ba.Tace iya salmai na kuka a daki wai jiya taga babanahar sunyi mgn dashi.Haisam yaja hannunta zuwa cikin dakin wurin iyasalmai.Haisam yasa wuya kafin ya lallashi iya salmai ta daina kuka ta fara amsa masa tambayoyin sa.Iya salmai ta bude baki ta fara musu bayani turyanturyan.Tace duk ranar kasuwa ina kai tallar zogale inazama tare da fulani masu sayar da nono.Muna lbr dasu har suke bani lbrn wani mutum bawan Allah wanda yanzu ya zama malaminsu shiyake koya musu karatun salla da basu iya ba saizuwansa garinsu.Suka cemin mutumin basu san takamaimai ko danasalin wanne gari bane don yaki fada.Yayo doguwar suma har an binne shi masu binne shi na juyawa sai su kuma fulanin rigarsu sukakawo gawa kusada wnn kabari sai suka gakabarin yana motsi, sai akace a tona aga ko meyesbd daga dukkan alamu yanzun aka rufe kabarinwata kila bai mutu ba doguwar suma yayi yanzu yafarka. Sun tonawasaiga mutum mai rai bai rasu ba yanasalati, ka garza dashi asibitin Babura wajenwatansa guda bayamgn mlm sule har sanyarsa yasayar yana sayawa mutumin magani.Watansa guda baya magana malam sule harsaniyarsa yasayar yana sayawa mutumin magani. Bayan ansallamesu dagaasibiti ya warke da ragas ya ce sunansa malam Garba ammabazai koma garinsu ba sbd yasan an gama zamanmakokinshiansan ya mutu zasu tsorata suce yayi fatalwa." IyaSalmai tashar6e da hawaye ta ce "Da a raina na kawo ko malam Habune sai na ji ance malam Garba sunansa.Na tambayesu ina ne garin su mutumin sai sukacebai fadi shiko dan wanne gari bane yaki fada sai ya ce yanarokarsu dasu rike shi su taimakeshi shi kuma zai dinga taya su dakiwo zaidinga koya musu krt.Aka gina masa bukkarsa a bayan gidan malamsule. MalamSule ya rike malam Garba tamkar dan uwansa suje kiwo taresuci abinci tare ya koya mana krt da daddare bayankowa yadawo daga kasuwa mutumin yana da kirki."Cikin zumudi Hanna ta ce "Daga nan sa akayiyaya?" Iya Salmai ta ce sai nabar maganar anan na mantada ita sbdzaiyi wuya ace malam Habu ne kuma bance susuffantaminyadda mutumin yake ba na dai tambayesu tanazuwa kasuwa wataran su nunamin shi, suka ce baya zuwa ko inakullumyana cikin riga. Wata rana wani mijin kawata yazoya sameniya ce yau yaje wata riga wajen kanwarsa da takeaure a rigar yaga wani mutum kamarsa daya da Malam Habu,jar natambaye shi yana dawa ko kani a Babban Mutumya ce minbashi da kowa. Sau 3 mijin kawar tawa idan yajerigar yake zuwa ya fadamin irin kamar mutumin da yake ganida malamHabu harta 6aci.Tafiyarsu maganar komai iri daya da malam Habu.Sai jiya nace muje rigar nan inga mutumin nan.Wallah ina zuwa saiga Mallam Habu." Na yanke jiki na fadi saiyazo yatasheni ya ce "Salmai lafiya?"Na sake tabbatarwa shine sai ya ce ina 'yar baba?,"Hanna ta rikke iya Salmai tana kuna tana cewa tashiki kaini gurin Babana In ganshi.Haisam ya rike baki kawai yana kallon ikonAllah sai kabbara yake yana cewa Allahu Akbar.Ya jawo hanna jikinsa yana lallashinta ta kwantarda hnkln ta yau komai dare zasu je su ganshi inshaAllah.Wada yace iya da kin lallaba shi ya dawo garin nan kun taho tare.Iya salami tace nayi2 yazo mu tafi yaki yace kumakada in fadawa kowa na ganshi yace baya son yasake irin rywr da yayi a baya tare da iya Abu da'ya'yanta shi zamansa a rigarnan yafi masa alheri dakwanciyar hnkl, daman hanne yakeji ya aiko a duba halin da take ciki ance 'yan uwan uwarta suntafi da ita niger.Shi kenan hnkln sa a kwance sai dai wani lkc idanya tuna ta zaiyi ta kuka har ya godewa Allah. Hanna ta girgiza kai tace babana kuwa kika ganiiya salmai? Kai bashi bane babana ya mutu,mutuwa 1 ce.Haism yace hanna karki kiyi mmk ikon Allah yawuce hk.Ana samun irin haka mutum yayi doguwar suma a binneshi ashe bai mutu ba, aga kabarin yana motsia tuno kuma mutum ya tashi ya ci gaba da ryw saidai wasu su kan ido ko kansu ya karkace ko bakinsu ya juye.Yana faruwa amma baefi a miliyan 10 baefi a samuirin haka 1 ba, zamuje mu gani Allah yasa shine hanna ki huta da koke-koken nan da kullum kikeyi na rashin mahaifinki.Iya salmai tace shine mana na ganshi har munyimgn dashi. Mlm habu ras yke babu inda ya lahantaa jikin sa.Haisam yace ai ikon Allah ne ba tare da ke mukaji a shirin INDA RANKA KA ba na FREEDOM RADIO akwaimutumin da aka binne shi sau 3 ana tonoshi ashebai mutu ba sukayi hira dashi shima ras yake bainda ya nakasa.hanna ta mike da sauri tana cewa ku taso mujejikinta rawayake kamar ta zama tsuntsuwa ta dira agaban mahaifinta.Haisam ya cewa shehu direba ya zauna shida wadazasuje su dawo.Haisam yana tukawa , hanna na gefensa, iya salmai na baya ta nuna hanya suna tafiya.Sun isa rigar suka iske bakkarsa babu kowa wanibafulatani yana biye da shanunsa suka tambaye shiko ina mlm garba sun leqa bunkarshi bayanan saiyace yanxun nan ya rabo dasu shi da mlm salesuna can kogi shanunsu suna shan ruwa. Ya kwatanta musu inda kogin yake suka nufa.Har suka isa surkukin da mota baza ta shiga basuka fara dabawa da kafa tun daga nan sukahango shanu suna shan ruwa da wasu mutaneguda 2 a zazzaune.Suna karaso wa mutanen nan na juyow sai ga fuskar malm habu tirra mura..fuskar mahaifinta ta sake gani, ta fada atsorace baba kaine kuwa? Ya matsa hawaye yace'yar baba nine.Suka rike juna sai kuka suke tamkar ransu zai fita.Yayin da farin ciki tamkar ya halakasu.Wohoho hasko minute zukatan wadannan bayin Allah.Uba da yarsa masu tsantsar son juna da shakuwa.Hanna tace baba kai ne uwata kaine ubana kanaraye a duniyar nan baka mutu ba kaki nemana aisai kazo in ganka kayimin bayani inya so sai kacekar in fadawa kowa. Mlm habu yace yi hkr 'yar baba da ace haka kawainazo miki tsorata zakiyi. Ko kuma ma ki rasa hnklnku bansan ta ina zan baiyana kai na gareku ba, dadai akace min kin bar hannu iya abu hakika nasankin fita daga kangi.Suka karasa cikin bukkasa inda suka zazzauna har mlm sule.Mlm habu ya zaiyane musu lbr kamar yadda fulaninnan suka gayawa iya salmai.Hanna ta bawa babanta lbrn halin rywr ta har zuwarana irin ta yau ya dinga hawaye daga karrshe yayihamdala ya mikawa haisam hannu suka gaisa yana ta shi masa albarka.Daga karshe hanna da haisam sunyi sunyi , juyindny nan akan yazo su tafi dashi kno yakikasancewar hanna tasan yana matukar son yajekasa mai tsarki wato makka sai tace baba makka fazamu wuce da kai. Tana ambaton makka sai yace indai makka ce zanjekunga sai inyi zamana acan in dinga ibada harAllah ya dauki raina, kujeku gama shirye shiryenku kuzo ku dauke ni ku kaini. Allah ya shi. Mukualbarka. Hanna ta nunawa haism ya tafi kawai yabarta ita zata zauna anan da babanta tunda bazai yarda ya bisu ba su tafi dashi ba. Dakyar haisam ,baba habu, mlm sule da iya salmai suka lallashe tata tashi suka tafi tana rusa kuka ita a wajenbabanta zata zauna. Ta bisu bisa sharadin zasujebabban mutum su kwana washegari in zasu tafizsu sake biyowa ta ganshi snn su wuce kazaure sai su wuce kano kuma duk bayan sati zata dingazuwa tana ganin mahaifinta.suna tahowa. Motahanna ta ware ta murnakamar zta zuba ruwa a kasa tasha. Taji zcyrta wsaikamar zata zuba a ksa tasha. Taji zuciyrta wasaitamkar bata taba jin bacin rai a rywr ta ba,haism yajiwani sabon farinciki sbd hannarsa nomore cry.Suna shiga babban mutum suka bullo ta kafar gidan iya abu har sun wuce hanna ta cewahaisanya dawo baya zata shiga ta gaishe da iya abu.Da farko haisam. Yaki sida iya salmai tasabaki snnya bar hanna, tace ya taho su shiga tare sukadunguma. Su duka da iya salmaicikin gidan.Suna shiga tsakar gidan suka ji yiim.a fuskarsu an watso musu tsummokarai.Wasu mata ne guda 2. Sun damko wata tsohuwazasu yi waje daita. Hanna ta jawo tsohuwar dagahannn matan tace ku lfy ina zaku kai ta, me tayimuku? Haisam ya tashi tsohuwar zaune yace iyamai ya faru tace ku taimakeni bayin Allah wadannaan mugayen matan zasu kashe ni wuyasuke bani.Hanna ta matso kusa tace ke wacece, kuma meyehadinki da su? Tsohuwar tace sunna Abuwa dagdana ne muka sayar yanzu kuma haya nake a cikiban biya kudin hy ba shine zasu kore ni sai hanna tace iyabu kece? Tce nice wacece nke gani kamarhanne. Hanna tace nice,ikon Allah iya bu kece kikazama haka, meya same ki a ido 1ya tsiyaye? Gakafrki 1 ma ta kumbura kamar jarka ciwon kafakike yi? Iya abu ta rushe da kuka, haisam yayimurmushi yace wai yanzu abun ce ta zama haka? Iya salmai tace abu ai tayi kyan gani tun watasadaka mai tsoka da wani mai kudi ya basu dubu 33 ita da abokin bararta ta alh bilya, kunsan kuturtartasa ta baiyana, matan da 'ya'yan duk sun watsekudi babu. Itam abu duk 'ya'yan nata sun zamayan iska matan da mazan, sun sayr da gidan uban yanzu hak haya take dn basu da gidan zama.Matan gdan suka ce sun sayar man da gida mukajitausaayinta muka sakata a dki 1 hay gashi yu wata2 bta biya mu ba 'ya'yan nata yan daba basujesunyo dabar ba sun biya mata.Wlh yau baza ta kwana a dakin nan ba saidai in ta shiga cikin rumbun nan mai gidan turuwa. Hannata bude baki zata roki matan iya salmai ta katse tatace 'yar baba barta ta kwana a rumbun tururuwarko kwana 1 ne taji idan da dadi,kin manta ranar daita da abokin bararta Alh bilya sukayi miki watsi dakayanki suka ce ki koma rumbu. Hisam yace haka akayi, ai kin bani lbrn yadda kuka yi, ta kwana kosau 1 ne taji.Iya abu ta rushe da kuka tana cewa yanzu yayaza'ayi mutum dan adam ace ya shiga wnn rumbummai tururuwa ya kwana.Iya salmai na kwasar kayan iya abu tana watsawa cikin rumbum tana cewa kwana 1 kawai zaki yikafin hanne tyi tnn zata samarmiki ki dinga kwana.Hanna taji hawayen tausayi ya zubomata tafitakofar gida tana hawaye.Haisam da iya salmai kuwa suna can suna lallashiniya abu tayi hkr ta kwana a gidan turuwar zuwa gobe. Iya abu ta rarrafa ta shiga rumbun tana rusakuka ta cewa duniya ta juya min baya yauna shiga3 na lalace. Haisaam da iya salmai suka fito kofrgida suka sami hanna suna tsaye da musbah dangidan iya abu.Kaca 2 da shi tmkar mahaukaci talauci tsantsa. Hnna ta gigiza kai tace musbah ya haka? Ya fasheda kuka yafara zaiyanawa hanna irin halin da sukeciki talauci da hau dabala'in da yake ta bibiyarsu yabata lbrn cewar sunyi aure sun kai matansu gidansuna zaune da iya abu.Iya abu ta fara yi musu masifa tana so ta gallaza musu su kuwa suka bijire mata, har wata rana sukatsiyayar mata da ido 1 daga karshe ma suka ficesuka fasa auran.Mu kum a tsakaninmu muka dinga fada akangidan,Matan su mahajana sun zama karuwai suma sukace nan gidan zasu dinga kawo maza mu kuma mukaki yadda akayi ta rigima daga karshe sai gidan akasayar muka raba kudin ba tare da iya abu ta sani badukmuka watse, yanzu sai tayi bara snn ta biyakudin haya. Ga wani ciwon kafa, kafarta takumbura kamar bokiti komai ya cakude mana. Hanna ta share hawaye tace a gidan iya salmai zankwana gobe dasafe ka tattaro min kanku kuzo kusameni kafin na tafi.Ya rakasu har mota yana soshe soshe yace tohanne bani na kashewa da daddare mana iyasalmai tace zai sha wiwi dare kenan. Hanna taciro 2k ta bashi tace musbak karka sha wani abunmaye kaci abinci ka sayawa mahaifiyarka abinci kakaimata.Ya dinga gdy da farin ciki.Har zasu shiga mota sai ga Alh bilya ya taho hannatace dasu haisam ga alh bilya ya taho hanna tace dasu haisam ga alh bilya bari na bashi sadaka takarsa wajensa ta zuba masa dubu 5 a kwananbararsa tace alh ga sadaka. Yace nagode Allah yakarba.Iya salmai ta matso kusa dashi tace hanne ce'yar gidan mlm habu, budurrwarka ta da mai dakinhaya.Ya sunkuyar da kai kasa dan kunya.iya salmai tasake cewa ina zakajene? Yace abu na biyowa mujebara ance za'abada sadakar abinci a kofar gidn mi gari iya salmai tace abu tana ciki kaayi sallama arumbun nan mai tururuwa zakaji ta amsa. Hanna tashiga mota cike da tausayinsa, iya salmai ma tazo tashiga, daman haisam yanaciki yan kallan su yagirgiza kai yaja motar suka tafi.A hanya hanna take cewa yanzu tun a dny Allah yake sakayya ba sai an mutu ba ko? Haisam yacekwarai kuwa shiyasa ake son mutum ya dingashirya alheri a rywr sa.Hanna tace Allah sarki yanzu dubi kudi irina alhbilya babu kamarsa a garin nan, dubi isa da mulkida rshin mutunci irin na iya abu yanzu sun zama a bamu dan dago-dago.Iya salmai taci gaba da basu lbrn irin bala'in da iyaabu da 'ya'yan ta suke ciki.Da sassafe sai ga iya abu da 'ya'yanta sun dira agidan iya salmai.Sun iske hanna da iya salmai suna shan koko da kosai bayan sun gaisa sai hanna tabi kowannan suda kallo 1 bayan 1, yamusti da sunan wani kaya.Duk sunyi kaca2 dasu kayan jikinsu dukkan sumatan da mazan, nan fa aka hau koke2. Kallonhanna suke tamkar sun sami hoto sbd kyawun datayi kamar wata gwal. Sai hanna ta shiga yi musu nasihohi tana basu shawarwari akan masukaruwanci, sce2 da shaye2 su dai na abu ne markyau. Takara da cew har da rashin ilimi yakedamunku babu arabi ba boko.Don haka su shiga mkrnt su koyi ktrn kur'ni suyaki jahilci. Daga karshe ta shaida musu zata bar musu kudi awajen iya salmai a hnkl a samu gida mai dakunadayawa a saya musu su koma su zauna su rungumiuwarsu snn suyi aure, tace zata bar musu kudi awajen iya salmai a hnkl a samu gida mai dakuna dayawaa a saya musu su koma su zauna su rungumi uwarsu snn suyi aure, tace zata basu kudi akai iyaabu asibitin kashi na kano ayi mata maganin ciwonkafa snn dukkan su zata basu jari kowa ya samu.tace zata basu kudi akai iyaabu asibitin kashi na kano ayi mata maganin ciwonkafa snn dukkan su zata basu jari kowa ya samusana'ar yi kada su kara barin iya abu tayi bara, saisuka fashe da kuka dukansu suna gdy. Iya abu nakuka tana cewa na shuka tsiya na girbi tsiya, na cuci kai na da 'ya'yana na hana su krt yau ga shisun tashi atutar babu,Hanna ki yafemin abun da nayi miki na yiwamahaifanki Allah ya jikan habi da habu.Iya salmai tace Allahu akbar albarkacin hanne yaumlm hbu ya samu addu'a da dadi ba'a taba yi masa ba. Haisam ne ya shigo ya sume su suna mgnr iyaabu na kwakwazon kuka tana nadama.Ya ce abu yi hkr haka duniya ta gada kaso nakaduniya ta kishi, sharri da jafa'I babu wandabakidora akan hanna ba sbd tana zuwa mkrnt kinbiduk gari kin fadin iskanci take zuwa ba karatu ba a karshe kalmar isknci sai ta dira akan 'ya'yanki matasuna aure ma suka kaso auran suka zama karuwai,Allah ya kiyaye gaba iya abu tace tone2 ma ai abarshi uncle haisam kuyi hkr dai Allah ya baku kubamu amma bala-n duniya wannene ban gani ba,Sakayya babu wcce Allah bai nunamin ba nida'ya'yana tun bayan tfyr hanne ban hutaba, zcy tabata hutaba saibaakinciki kala2. Daga karshe iyaabu da 'ya'yanta suka tafi da kudin da hannataraba musu suna gdy.Hnna da iya salmai da wada suka zauna suna lissafi, hanna ta bayar da kudin gidan da za'a kaaiwamaigari a sayawa su iya abu.Sannan ta dauko kudi mai yawa ta bawa iya salmaitace nata ne ta zauna a gida ta dinga cin kaza daabinci mai dadi tadaina zuwa kasuwa talla, sati nasama za'ayi bikin wada ta bada kudin komai wanda za'a bukata na hidimar bikin.Ta shaidawa iya salmai cewar nan da 'yan watanniza'a gma gina gidaje zata zo ta dauketa ita da wadada matarsa su kaura kano, katafariyar supermarket zata bude shine takeson wda ya zaunamata a kantin yana kula da wajen. Murna tasa iya salmai kuka sai juya makudan kudinda hanna ta basu takeyi tana ta gdy. Haisam da hanna da direbansu sun fito dagababban mutum sai sukanufi rigar damlm habuyake, sun iske shi bai fita kiwo ba yana jiranisowarsu.Bayan sun gaisa haisam yayi masa bayani nan dasati 3 za'a gama biza zasu zo su dauke shi su tafi makka.Sai farinciki ya rufe mlm habu kudi mai yawa sukjibge masa, hannasai zrowa take tana tulewa agabans shi kuma hanata yake yana cewa 'yar babakudin sun isa haka mai zan saya a rigr nan dawadannan makudan kudi. Shimamlm sule sun shiga har gdansa sun rabamusu kudi shi da matansa sai gdy suke sunamurna.Aka hadu a gidan akayi ta hira har har hira tayi hirahanna ta gane ashe mlm sule kanin mlm sale netsohon daya bata abin busa a wajen kiwo tun tan yrny.Aka rakata gidan marigayi mlm sale tayiwa iyalansaalheri mai yawa.Dakyar haisam ya banbaro hanna daga rigar nan,bada son ranta ba ta baro mahifinta.'Yan rigr suka fito kusan gaba daynsu wahjen motar su hanna suna daga musu hannu. Shehu yajmotar suka tafi. Hanna zata fara hawaye sbd zatatafi ta bar mahaifinta sai taga hasam yana harararta,ya tsreta da ido baya ko kirfatwa sai ta wayance tafasa yin kukan tahau yi masa hira, haisam yayimurmushi yace hanna kuka sunanki daga yau. Hanna ta kwanto a jikinsa ta kashe murya tacekukan farinciki zanyi yaya, daka kbarni nayi, kadanfa xan danyi hawaye daya 2 shikenan sai inyi shiru.Suka kyalkyle da dry dukkansu.Haisam yace kinyi digiri a kuka har kaiyadewa kikeyi kenan.basu tsaya a ko ina ba sai a garin kzaure kofargidan uwar biyu. Suka iske ta a tskr gida tana sakindaanwaken siyarwa.Ciwon kafa ya hana ta aiki a mkrnt sai a gida takesiyar da binci kala2 na sfe daban na rana daban nadare daban. Uwarbiyu ta bude baki tana mmkn ganin haisam dahanna.Haisam yayi dry yace uwarbiyu hanna matata ce,munzo mu gaisheki ne.tayi hawye tace har babbanmutum naje neman hanna da. Naji ance mahaifinkiya rasu inyi miki ta'aziyya, inga yaya zamanki yake da iya abu inda hali in daukoki kizomu zauna tare,sai aka ce mun kin koma niger.Hanna tace Allah sarki uwata ta kaina nima ina tnnninki kullum.Ta shimfida musu tabarma a gindin wata bishiyamai iska a tsakar gidanta, ta zubo musu ruwa da danwake ta kawo musu snn tazo ta zauna sukagaisa.Bayan sun gaisa sai hanna ta kwashe lbrnmahaifinta ta fadawa uwarbiyu cewar bai rasu bayan nan da ransa. Uwar biyu tayi murna ta tayahnna murna matuka. Haisam ya dubi agogon dake daure a hannunsayace yanzu 12:30 a kano nakeso muyi sallarazahaar muci abinci a gurguje mukazo mu gaisheki, snn idan ba zaki damu ba hanna tana so tazo tadaukeki ki koma kano da zama tare da ita ki barwahalhallunnan. Yanzu haka tasa a gina muku gida a kusa da nata ki koma ke da iya salmai. Uwarbiyuta fashe da kukan murna, kudi dumus taga hannata debo daga jakarta ta ajiye mata a gaba tayi tagdy ta rako su har wajen mota sukaa shiga sukatafi. Suna isa jano basu tsaya a ko ina ba sai a filin jirginsama haisam ya cewa shehu direba ya tfi gida damotar zasu dawo.Bayn sun sayi tikiti sukayi salla sukaci binci. Filinjirgin. Sun isa abj da yamma, direban ofis dinhaisam yazo yadaukesu wato wajen sayar da motocinsa.Kai tsye ya wuce dasu katafaren hotel dinnan watosheraton hotel.Hakika wnn hutu ya ywa masoya nan 2 dadi fiyedana ksashen wajen da sukaje.Sbd hnkln hanna a kwance yake, sai farin ciki ya rufeta idan ta tunamhifinta nanan a raye bai mutuba har tsalle take akn gado tadiro ksa ta fada kanhaisam tana murna.Haisam sai ya zauna yana kallonta kawi yanamurmushi domin farincikinta shine frin cikinsa.Da yamma suna saukowa wajen swimming pool suyi ta wanka da safe kuma sai direban ofishinhaisam yazo ya duke su suyi ta yawo a cikin gariwaje2 na hutawa da waje ciye2 makulshe, gidjen'yan uwnsa da bokan arziki dun sun zazzaga hkake ta bawa hanna kyututtuka.$sunje wjen sayarda motocin haisam wajen ya kawata ga motoci galla galla.kamar da wasa hanna ta zabarwa mahaifintawata galleliyar mota tace idan ya dawo daga saudiazata bashi, maimakon tayi gdy haisam ne yakemata gdy sbd yaji dadi sosai yau hanna ta tambayeshi abinsa.Kwanan su 8 a abj snn suka hau jirgi suka dawo kano.A daren da suka dawo ramlah zata haihu.Haisam da hanna suka rakata sibiti, ta haifozukekiyar 'yarta mai kama da ubanta sak.Bayan kwana 2 haisam ya tambayi ramlah wanesuna za'a sawa 'yar, abin mmk sai tace asa mata sunan hanna. Hanna tayi farinciki matuka gatajininta ya hadu da 'yar barci ne kawai yake rabohanna daha dakin ramlah wjen 'yar jaririya.ranar suna anyi bidiri naira ta sha kashi, an kashenaira, an lika naira.Taron mata kuwa harda wanda ba'a gayyace su ba. Kasancewar ramlah yanzu ta zama mai jama'a anata sanarwa a redio sai jama'a masu sauraronshirinta suka nemo inda take suna zuwa tayatamurna.Saboda hidimomin suna Hanna d Haisam basusamu dama sunje sunga Malam Habu a cikin satinnan ba, sai sati na sama Haisam ya fara cuku-cukunnemar bizar tafiya Makkah. Ya ba Hanna hkr ta bariin an samu bizar tafiya sai suje su dauko shi su wuce. Suna cin abinci suna hira suka sanarwa daRamla halin dake ciki cewar mahaifin Hanna bairasu ba, tayi mmk kwarai ta taya hanna murnasosai, sun shaida mata nan da sati mai zuwa zasu jesu dauko shi su kai shi Saudiya.Haisam da Hanna sunje gidansu Haisam sunshaidawa Alhj da Hjyr Haisam lbrn mahaifin Hanna,d farko mahaifin Haisam d dry ya tuntsire sbd lbrnyayi masa kama d tatsuniya, mahaifiyar Haisam cemusu tayi yaushe muka zama kakannin ku kukemana wasan kaka?"Sai da suka ga d gaske suke har da rantsuwaHaisam yake ya shaida musu zasu je su dauko shisati mai zuwa su raka shi Saudia don ya ce ba zaibiyo su yana zauna anan ba, sun sha mmk sun tayaHanna murna kwarai da gaske."Bayan komai d komai na tafiya ya kammala Haisamd Hanna suka shirya suka nufi rigar da Malam Habuyake suna isa baba 6ata lkc mai yawa suka daukoshi suka taho dashi Kano.Malam Habu ya sha mmk ganin gidan da Hanna yabude baki kawai yana kallon kayan alatu, a 6angaren Hanna aka sauke shi a dakin kasa.Ramla tazo ta gaishe shi sai da fuskarta ta fadomasa arai, ya hangota lkcn da tazo taci masamutunci akan Hanna ta rabu da Haisma, ya jinjina aransa ya ce rayuwa kenan yau gata a durkushe agabansa tana gaishe shi cikin girmamawa.Ya kar6i 'yarta yayi mata addu'a daga karshe yanuna farin cikinsa da aka sa sunan Hanna. Da daddare mahaifin Haisam suka suka gaishe shisuka kawo masa farfesun dagwalan kaji da juiceskala-kala. Bayan zuwansa da kwana 3 suka nufikasa mai tsarki. Kwannan su Hanna 10 a makka. Bayan sun tabbatasun samarwa mallam Gabu gidan zama wadataccekudi mai dimbin yawa wanda zai ishe shi ci da shada sutura sun daukar masa ma'aikaci daya da zaidinga kuka da shi, wankin kayansa da kuma rakashi duk inda zai je kamar,,, Madina ko Jedda duk dai inda yake so ya je. Mallam Habu yayi matukar jin dadin da ya bude isoya ganshi cikin wannan kasa mai tsarki ga shi gaKa'aba. Zai je duk inda ya ke so a cikin kasar Makkah babumai kama shi sbd sun yi masa igama ma'anatakarda izinin zama a kasar har lkcn aikin Hajji.Bayan su Hanna sun dawo Nijeriya ba dadewajarabawar Jamb dinsu ta fito kai tsaye suka bataMedeicne sbd points dinta ta cancani idn course dinda yafi Medicine a bata, murna a wajen Haisam abinbaya musultuwa har ya fi Hanna murna. Haisam ya taya ta yin registration, bayanrigestration ba dadewa suka fara lectures. Karatutukuru ta sa a gaba musamman ma idan ta tuna irinyadda krtn Medicine yake da mahimmanci a wajentaimakon al'umma. Tana da burin ta ga tanataimakon talakawa a rayuwarta. Ginin da ake yiwa Hanna yayi nisa, duk da ba akare ginin ba amma zaka san katafaren gim ne maikyan gaske. Shinfidedan masallaci, daya 6angaren makarantarIslamiya ta matan aure da yara ga bandaki nan agefe. Can baya kuma wata kofa ce inka shiga zaka tararda gidaje iri daya guda 2, masu dauke da katafarenfalo da kunanan barci uku-uku kowannensu dabandakinsa a ciki da kicin. Haisam ya sayawa Hanna da Ramla wani katon fili aAhmadu Bello way inda kowacce a cikin kudinta yake gina mata katafaren kanti kamar yadda Hannata ce tana son super market a kusa da nan ake ginamata wani ofis na tallafawa marayun yara. A kusa da shi katafaren kantina biyu ne na Ramla,daya na sayar da kayan Senegal dinkakku (readymade) daya kuma na sayar da takalmin dajakunkuna 'yan waje. HaiRamHannah! HaiRamHannah!!Bayan an gama ginin an kawata shi da fitulu da tilessai akayo odar kaya wasu daga kasar waje wasudaga kamfononin nan kasar.Wada ya gigice a lkcn da Hanna d Haisam sukakaishi katafariyar super market din, anan akace yadinga kula da ma'aikatan wajen yana sa'ido akanyadda ake gudanar da cinikin. Kasancewar yayimkrnt sakandire ya iya krt da rubutu. Hanna ta kara masa da cewa 'yanzu baka san gari ba kumabaka iya mota ba za'a dinga kaika ana dauko ka damotar kantin, nan gaba zan saya maka taka takanka." Wada yana ta murna yana gdy haka Iya Salmai dauwar biyu sunsha koke-koke dn murna suna tagdy." Wada da matarsa Jiddau a gida daya, IyaSalmai da Uwa biyu a gida daya kowacce a dakidaya, daki daya ne babu kowa aka kulle shi. Suci susha suyi wanka a kunna musu kalloshikenan aikinsu suyi ta hira. Wani lkc Iya Salmai tace azo a danno mata lmbr malm Habu a Makkah sugaisa. An huda kofa wacce zata kaika gidansuHanna kullm Hanna sai ta shigo gidan tsofaffin nanta taya su hira bayan ta taso daga mkrnt, gaba dayansu suna cikin tsananin farin ciki da nishadi koba'a gaya maka idan ka kalle su. Hanna taji dadi ta gama jarabawa a lkcn d ake tafiyaaikin hajji don haka ta shaidawa Haisam tana sotaje Makka ita da Uwar biyu da Iya Salmai suje suhadu da mahaifinta suyi Hajji gaba daya don itataimaka masa kada yasha wuya. Haisam ya amsamata da cewa babu komai zaiyi kokari yasa a neno musu biza su dukka gidan ma sai ma sai su tafi, harshi da RamlaDa 'yarta Hanna, da Wada da matarsa da gaba daya'yan aikin gidan mata d maza. Haka kuwa akayi,suka dunguma suka dira a kasa mai tsarki kwatam!Malm Habu ya gansu nnfa murna ta hargitse. Kamaryadda su Hanna suka yi aikin Hajji waccan shekarar cikin sauki haka wannan shekarar ma, motakatuwa da direba aka aikowa Haisam daga gidnambassodor. Bayan an sauko daga arfat lfy, sai suka dinga shigakasuwanni ana ta siyayyar tsaraba. Makudan kudinda Haisam ya rarrabawa dukkaninsu kowa ya yiwa'yan uwansa tsaraba. Kowa yaji dadin tafiyar nansosai da sosai. Haisam da Hanna d Ramla ne suka shiga 6angarenMalam Habu dn su gaishe shi da sassafe.Suna zaune suna 'yar hira saiga uwar biyu da IyaSalmai suma daga dakinsu sun shigo don su gaisheda Alhj Habu aka hadu ana ta hira da wasa dadariya. Hanna ta ce "Baba da kai zamu tafi fa tunda yanzukayi umara sau da yawa ka yi aikin Hajji sai mukoma gida." Alh. Habu ya girgiza kai ya ce "yarbaba ki barini kawai inyi zamana daman ku kadainake dasu a Nigeria kuma gaku nan akai-akaikuna zuwa gara inyi zamana inci gaba da ibadata hr lkcn mutuwa anan." Hanna ta ce "Haba babakaso ka mutu babu aure bayan ga masoyiyarka nanan na jiranka ka dawo ka aureta." Alh Habu ya ceda Hanna ke 'yar baba bana son shakiyanci waceirin masoyiyata, wacce masoyiyata kuma?Gaba daya aka sa dry. Hanna ta ce "Baba har zaka manta tsohuwar matar'yar uwarka, jininka Iya Salmai a tuna baya manababa a koma ayi aure." Haisam ya ce "Baba Hannadai nason ayi tuwona maina ga uwa ga uba, Baba aduba wannan al'amarin."Malam Habu yayi murmushi ya ce "Kaima tayatakake?"Kyale 'yar baba tsokanarmu take yi Salmai dince tace mata tana so ta yi aure?"Iya Saimai sai yanzu tasa baki da murmushi kawai take yi ta ce "Da dai na gama aure tun daga kankaamma yanzu da ke kaine ai bana ce a'a ba.Soyayya ai bata tsufa."Hanna ta rangada gud'a ta ce "Ai an gama dauraaure sadaki kawai zan dauko in biya da Riyad mazan biya kudin Makka. "Uwar biyu tayi dry ta ce "Lallai wannan aure bakuAlh ne don a makka aka kullo shi.Allah ya sanya alheri ya ba da zaman lafiya."Hanna ta ce "Iya uwar biyu ko kema in tuno mikibaya ne?"Ta ce "Ban gane ba?" Hanna ta ce " ko ke ma zaki zama amarya iya salmaiku zama ku biyu a daura dukka rana daya tundagidanku daya tuwona maina kenan."Gaba daya aka kece da dry.Haisam ya ce "Lallai har kin yiwa iya Salmai kishiyatun kafin ta tare." Hanna ta ce "Ai itama tsohowar syy ce tun a lkcn datake kaini gida daga mkrnt t fada mun, ai shimaBaban ya sani, sunso dai-daita ya ce mata masifariya Abu ce kawai zaya hana ya aureta."Iya Salmai tayi caraf taace "ni da za'a yi haka ma danayi murna sbd ni a rayuwata ina son kishiya, bana kyamar kishiya ko Abu aini nasa dole ya aurota."Hanna ta dauko turare tana fesa musu su dukaukun wai amare da angonsu."Wannan abu ya yiwa kowa dadi ba kamar Hanna.Ramla da Haisam sunsha dry har sun godewa Allah.Yanzu Mlm Habu ya yarda zai biyo su su dawo Nigeria.Haisam ya shaida masa an nadashi matsayinlimamin masallacin da Hanna ta gina daman sunasaaka sawa Islamiyyar ABUBUKAR IMAM ISLAMIYYA.Sun dungumo gaba 1 sun dawo nigeria sunadawowa da sati 2 bayan uwarbiyu taje kazaure tashaidawa 'yan uwnta ta dawo daga makka ta rabamasu tsaraba saita shaida musu wnn abun mmkabun murna cewa zata auri mlm Habu babanhanna, Don haka ranar jumu'a 'yan uwan uwar biyuwaliyanta suka zo aka hadu da haisam da 'yanaikin gidan suka taru aka daura auren iya salmai damlm habu bayan an shafa aka daura auren uwarbiyu da mlm habu wnn abu yayi kyau aka rabagoro da alewa aka watse,Don haka ranar jumu'a 'yan uwan uwar biyuwaliyanta suka zo aka hadu da haisam da 'yanaikin gidan suka taru aka daura auren iya salmai damlm habu bayan an shafa aka daura auren uwarbiyu da mlm habu wnn abu yayi kyau aka rabagoro da alewa aka watse. Daya dakin na kulle aka budewa ango habu yashiga gana amarensa a gefe.Ko kofar gida mlm habu bai cika fita ba.Yana gida yana shan Ac yaci kaji yasha juice daabinci kala2 idan lkcn salla yayi yayi taku kadanzuwa masallaci ya shiga yaja jama'a sallah, da daddare kuma ya koyawa maza magidanta krtnalkur'ani mai girma.Mlm habu yayi shar dashi ya girgije duk tsufan yaragu daman ashe wahala tafi tsufan yawa.Haka uwarbiyu da iya salmai sunyi shar kamar basune wandannan tsofafin ba, kayansu kullum iri 1 hanna take dinko musu. Mkrntr islamiyya a hnkl a hnkl ta cika makil dadalibai yara da manya.Kullum da yamma yara ne suke zuwa , ranar asabarba lahadi kuma manyan matan aure suke zuwa dasafe 10-12.Manyan malamai masana alkur'ani da hadisai, kawa'idi, fikihu da dai sauransu daban2 su sukekoyarwa a mkrntr.Ramlah da hanna suma sun shiga mkrntr.Iya slmai da uwar biyu ma ba'a barsu a baya suntashi haikan neman ilimi dan da basu iya komai bayanzu kuwa gashi komai dalla2 suna koya. Matasan yan mata ne suke ta tururuwar zuwawajen ramlah akam matsalolin da suka damesuakan soyayya. Ramlh na kokarin warware masu tahanyar basu shawara, wata tambayar idan sukayimata sai ta sadasu da hanna tana hanin hanna zatafita sanin amsar sbd ta taba crossing irin wnn ryw so zata fita sanin amsar.wani lokaci har haisamyakan taimakawa rmlah wajen amsa wasutambayoyin. aji na musmman ramla da hanna sukaware a mkrntr isamiyya lkcn da babu mkrnt zamada matasa suna wayar musu kai akn mececesoyayya. Duk sanda ramlah take gudanar da shirinta hannace ta farko da tke fara bugo waya ta bada tatagudummawar a gidan radiyo kafin ta fara gudanarda shirinta sai tace fatn alheri ga haisam da hanna. Wata rana hanna ta sako kai zuwa cikin gidaniyayenta ta iske wada yana yiwa tsofaffin nan tsiyayana cewa wai ku yanzu bakwa iya cin abinci saikuna korawa da juice , katan 1 baya yi muku satiguda, ba'afi kwana 5 fa na kawo muku wancankwalin har ya kare, musmman iya salmai ana dauke wuta kafin a tashi inji sai kaji tana subhanaAllahibanason dubu wlh a rywta, koda a babban mutumya kike yi ke da ko wuta bakiji a gidanki ba.Uwar biyu kuwa ita dai a kunna mata sattelite tanakallon tana tsalle akan kujera tana dry,Su baba habu kuwa shi dai asha AC a figi naman kaza.Hanna ta talli keyar wada ya zabuwa ya juya dasauri, sai yaga hanna. Iya salmai tace gara da Allahya kawo ki gashi nan ya zamar damu kamarkakaninsa wai tsiya yake yi mana.Hanna tace wada banason irin haka meye don sun shanye kantan din juice a sti, daga yau katan gomazaka dinga dauko musu daga kanti yan karewa kadauko wasu katan 10.Kake yi musu tsiya inaa kai nan nan matarka taceka kunna mata AC har riga ka cire ka jwo kujeraaka hu ka ballo murfin AC zaka girgideta Allah ya kawoni gidan na nuna makaa inda zaka matsa aremote ka kunna. Wai kai a dole ka nunawaamaryarka kai dan birni ne zaka burgeta.To gsky karka kara yiwa iyayena haka wlh kokayan kantin duka suke zo zansa a kwaso musudon Wa nake sana'ar? Dadi ya kashe tsofaffin nan saka hau shiwa hanna albarka. Allah ya albarkaci sana'ar hanna a shekara ta sakebude wata super market dan a zoo rd komai hannatasawa hannu na kasuwanci sai kaga kamarfarashi yana ta hauhawa riba tsibubu Allah ya dubizuciyar hanna yana ta buda mata ita kuwa bat gjyda bayarwa ga iyayenta da 'yanuwanta talakawa na niger dana babban mutum da duk al'ummarannabi da suke neman taimako.Yara da dama hanna ta dauki nauyin karatunsu,da yawa ta dau nauyin yi musu aure da yawa tabiya musu makka.Wata rana haisam ya dawo daga wajenhidimominsa da yamma kai tsaye bangaransa ya nufa don ya watsa ruwa yaji sanyi a jiknsa kafin yafito lambun da yake zama yayi hira da matansakullum da yamma.Abun mmk sai yake jiyo ana yin wata busa maidadin gaske wacce tayi masa kama da wata busada yake matukar so a rywr sa. Yayi sauri ya bude labulan windon dakin sa ya lekasashan da busar ke tashi, sai ya hango hannazaune cikin lambu tana busa abin busarta.Cikin sauri ya fada bandaki ya watsa ruwa bayanya shirya ya fito ya nufi cikin lambu inda hannatake. Ya lallabo ta bayanta ba tare data sani ba, ya tsayacak kusan minti 10 yana sauraranta , ya kare matakallo tsaf wuyanta ya ganta sanye da tsakiyoyinnan nata.Ya zagayo ya durkusa a gabanta yana kallon dige- digen da tayi da kwalli a fuskarta, ta dube shi tayi murmushi ta sunkuyar da kai kasa.Haisan yace lallai yau kin tuna baya kuma kin sosomin wani abu mai muhimmanci da yake cikinkundin tahirin rywta. Su duka suakyi dariya.Haisam ya mike tsaye ya jawo wata kujera ya zaunayacr cigba da busrki kuma kiyimin wakar ina sauraran ki hannata mike tsaye ta kara tsukedanmararta ta kugu snn ta koma ta. Zauna su dukasuka kwashe da dariya, ta kaikace ta fara busa tanarero wakar kiwo kamar yadda takeyi masa da.Haisam yayi shiru yana kallonta yayin dazuciyarsata harba can ta tunomasa baya wto ranar da aka fara kawo hanna mkrnt, da bayan rabuwarsda ita, da haln day shiga bayan rabuwrsu da irinbusar da yakeyi idan tnn ninta yayi masa yawa.Bai ankara ba sai ya ga hannatana hawaye itamababu abindataketunawa sai lkcn da mlm suleyabata wnn abun busar da kuma lkcn da haisam yake sata tayimasa busa.Hanna takifakaiakan cinyars ta saka kuka, ya miketsaye ya jawota jikins ya rungumeta sai shimakwalla ta far zubow dg idanuwansa.Ya laluba damarar da tayi a kugunt yace hannameye wnn nakejia kugunki kamar maciji? Tace ba maciji bane mayafina ne, suka kwashe da dry,haisam yasa hannu a aljihunsaya ciro wni abu adaure a bakr leda ya mikawa hanna, takarba cikinsauri takwance ta duba, saitga wata 'yar karamarrigar nono mai kyau.Ta dubi haism alamar bata gane ba, tace wnn fa? Yace kara kallonta di sosai ki Tuna baya, hanna tayishiru tana. Tnn, saihaism yace tuno ke da nusaibada rauda a wajan mai kanti a mkrtn? Tce laa shinekake ajiye da ita har yanzu.Haism yace ai duk wani abu dya shfeki hnna banamantawa dashi sbd muhimmancinki a rywta. Sita rungumeshi sukakoma suka zauna, sukaci gaba dabusa abin busar tare. Kwanci tashi hanna tayi nis. Kartun likita. (Medicine)sun gama shekaru 3 a BUK an turasu teachinghospital na Aminu kano don yin clinicals, sai yanzuhanna tasami ciki. Wai wai zo kuga tarairaya amurna wajen baba haisam.Duk mutuncin nusaiba da yake gani fur ya hana hanna taje ta raka ta hada-hadar kanfen din zabe,sunaa sosu zarce takarar gwanna.Yace shi dai saiind karfinsa ya kare amma hannabazi barta ba sbd dan cikin zai wahala da itakantaa. Zabe ya doso haisan yayi iya kokarinsawajen taya mai girma gwamna yakin neman zabe. Kasancewar haisam shine kano, yasan 'yan kano,yana son kanawa, kanawa suna sonsa shidahanna da ramlah sbd irin gudunmawar da sukebwa kanawa, kanwa sun ams kiran haisam sunsake zabar mijin nusaiba a matsayin gwamnankano karo na 2. Mai giram gwamna da kansa yajinjinawa haisam ya kudiri niyyar saiya linkwahaisam tara ta arziki, fiye da yadda haisam yayimasa.Haka kuwa akayisaidai kwangila mai tsoka batataso ba amma haisam yake bawa ta dariruwanmiliyoyi kuma a biyashi da zara ya gama, haisam kano kenan , arziki ya dada bunkasa yanzu haisamyaso yafi mahifnsa kudi dan yafi yayansa habibkudi shine ma yake basu kudi.Hanna ta haifi santalelen danta kyakykyawamai kama da babansa amma ya dauko farar fataruwarsa, hanna tace asa masa sunan babantabubukar ana kiransa da walid.Bayan haihuwar walid da wata 3 ramlh tahaifi da namiji shima mai kama da babansa aka saka masasunan mahifinta shitu ake kiransa khalil.Hanna ta tashi tukuru tana ta karatu bata damatsala wajen rainon walid tunda ga iya salmai nanda uwar 2 sun rike mata shi, nono ne kawai taakezagayowa ta bashi takomaa karatu har ya isa yaye ta yayeshi.Tafitfyhnn ta gama karatun likita da bautar kasa, tasake haifar 'yan biyu mace da namiji masu kama dahanna sak.........Hanna ta gama karatun likita da bautar kasa, tasake haifar 'yan biyu mace da namiji masu kama dahanna sak, hanna taroki haisam da asa mususunan haisam da ramlah da gudu ya mincewabakatarta, hai Ran hannah kenan, tubarkallaalhmdl, iyali sun hadu gida yayi albarka 'yan dugul dugul yara zaka iske a farfajiyar gidan suna ta gujegujensu haism na tsakiyarsu yana tayasu ball. Drhanna haisam abubakar ta. Cika burinta ta zamacikekkiyar likita ta sami damar ta taimakawaal'umma ta far iki a Aminu kano sai taga gwra takoma karatu ta karantobangaren mata wato (gaenea) A B U zaria tayi karatun shekara 4 a indata zama consultant gyanea doctor, abunda haisamya fara yi shine yabude mata asibiti su suke kuladamarasa lfy a asibitin.Mi girmanusaiba dai suna nan suna ta siysa tafi tfytakarar shugaban kasa mai gidanta yaa tsaya. Haisam dai na nan na taya su yakin neman zabe.Allah cikin ikon sa y lashe zaben shgabancin kasarnig, nusaiba a matsayin first lady. Mukami mai tsojata zabarwa kawarta hanna, guest wat? Ministerlafiya tasa mai gidanta ya nada DR hanna haisamabubakar imam ('yar baba) an duba cancanta hanna tacancanci a bata.Haisam kuma aka bashi jakadan nigeria dake kasaramerica (ambassardo of U S A). Hanna baza ta iyakaura america gaba daya ba sbd aikinta,hakaramlah ma bata so ta tafi tabar aikinta na gidanrediyon data keyi. Gashi har haisam da hanna da ita ramlah sunakokarin bude radio nasu na kansu mai sun Hai RamHannah radio station.Ka-ka-ka-ka to yanxu yaya za'ayi wnn zamankenan haisam na america, hanna tana abj aktafaren gidan gwamnatin da akabata a unguwar ministoci. Ga ramlha a kano tana bude gidanrediyon kanta don watsa shirye shiryenta.Daga karshe shawara da aka shirya itace hisamdaramlah da yaransu duka 5 din wato hanna, wald,khalil, haisam da ralmah duuka zasu koma americada karatun yaran gaba 1. Snn za'a bude gidan radiyo a zuba kwararun ma'aikata suci gaba dafadakar da al'umma snn duksati kamar yaddaramlah ta saba gudanar da shirinta. Zata vigaba dagudanar wa ammata hanyar wayar tangarahu za'adinga jonata da gidn radiyon amma fa wnn wayartangarahun tr akejin murya hakakuma take jin tambayoyin da akeyimata take amsawa. Wanilokaci kuma ana jinta a radiyo muryar america, idantaje london kuma ana hira da ita a BBC london.Ita dai burinta ta fadakar da mata akansoyayya dazamantakewar aure duk mahakurci yana tare dasamu itama ta shiga mkrnt a america tan yin masters akan mass com.Ci gab wai bera akan cinyar mage yan kallontalabijin da remote a hannunsa yana matsawa injiwata mai iya mgn.Gaba daya gidan haisam kacokan an mallakawamlm habu kyauta shi da matansa. Iya salama abangaren hanna iya uwar biyu a bangaren ramlah mlm habu shine maigida a bangaren uncle haisam.Masu gadi damasu bawa fulawa ruwa da masu dafabinci da direba duk sunci gaba da aiki a karkashinmlm habu yana biyansu da dimbin. Kudin da 'yarbaba take jubgo masa. Hakika mlm habu ko da alahira ya samu haka lallai ya samu rahama, irin wnna daula abin sai wanda ya gani sai ma kunhango shi cikin jibgigiyar mota mai aC ana tukashiya kame owners yasha jibga jibgan kaya naalfarma, wayyo ba a fidda rai da rahamar ubangjiji.Raban mutum gudu yke yazo ya same shi fiye dayadda mutum yake nemansa. Allah kayi mana arziki ta hanyar halak amin. Ku haskomin iya abu an guntike mata kafa 1 aasibitin da sandina 2 take dogarawa. A yu dayammaitaa da 'ya'yanta duka suka dira a kofargidan hanna da kwantance da tambaya suka ganogidan da kyar masu gadi suka barsu suka shigaciki suna shigowa sukaiske mlm habu da matansa 2 a zaune akan katuwar darduma sun shan kyanmarmari iri2. Nan kagagigicewa da razana a wajeniya aabu da 'ya'yanta a guje suka ruga ba tare dasun san kofar fita ba.Sandunan iya bu suka zube ksagashi idon 1 netake dan kyallarawa. Ta fadi fuk a kasa tana ihu tana kururuwa wai yaugata a lahira a gidan matattu ga mlm habu ga uwar2 da iya salmai ashe sama su salmai duk sun mutu,yau gata a gidansu na laahira azo afita da ita dagakiyama.Kuzo kuga dry harda faduwa a wajan mlm habu da matansa, bayan dryr da taci karfin su ta lafamlmhabu ya kwallawa mai gadi kira yace ya shiga cikinlungunan gidan ya harhado kanmutanan nan dasuka ruga aace suzo ba fatalwa suka gani bamutane ne. Iya salmai ce ta taso tazo wajen iya abutaake darkushe tana kururuwa ta fara yi mata bayani akan ta kwantar da hnkln ta duniya takecikin mutane 'yan uwanta ba matattuba. Bayan duk n hado kansu sunzosun zauna agabanmlm habu gaba dayan su a firgice suke kamar kacekule suce cas, is makerketa suke musamman mamatan sunfi tsorta.Mlm habu yayi gyaran murya, yayi bismillah, yayihamdala snn ya dora musu da bayani ya baus lbr kakaf aabinda ya faru dashi tun dag ranar ya akakai shi kabari har rana irin ta yau, ya shaiida musuya auri iya salmai da uwar biyu. Sai duk suka dukuka suna bayyan rashin jin dadinsu akan baindayayi musu na rashin damuwa dasu koda wasahanna bata taba fadamusu ba kuma tana zuwa garin, saidai suji a gari aana fadin wai wai mlmhabu bai rasu ba ana ganinsa a gidan hanneammasu basu yadda ba sun dauka zancen 'yan gari nedon ba'a mutuwa a dawo ashe da gaske ne. Mlmhabu yayi murmushi yace kuyi hkr nina gargadihnne karta fada muku, mma kada kuga laifinta sbd. Cikin ku bbu wanda n tafi na bari yanakaramidukkanku na ciyar daku, na shayr daku, na tifatardaku, na saka ku mkrnt kuna gidan mzjenkusanda na barku fan haka nsan bani nuyin kowa akaina.Abu kuwa tuni kinyr dani, bola ma ta fini daraja,kin gaji kinfi son in mutu ki huta da wahala daninima har nazonafi son haka, yayanki gaba dya sunrainani kamar ba nine na haifesu ba ban isa inasaku ba, ban isa in hanaku ba sbd uwrkutanunamuku bani da amfani. Bakin cikin ryw da wulakanci babu wanda bamugani ba ni da marainiyar yata 'yar baba.Na samu lbrn irin rashin mutuncin daku kadingayiwa 'yrbaba tun daga wajan raban gadosaidai ta fitadaga dakin ta koma runbu saida akabiyamata kudin haya, tazo ta rasa mai bata abinci duk gaarin sai salmai itama da takeci daa kyar.Abu yanzu wa duniya ta waya? Duk abinda kikashuka shi kike girba,Nasha wuya ainun azamana daku naga bakincikinaga rashin mutunci kala kala, haka mahaifiyarhanne habi har ta koma gamahalaccinta tana shan azabarki abu bare hanne babu wurar da bata sh badan da wuya bata kisa da tuni tamutu .Ba gori ba, yanzu gidan da kuke zaune wacece tasiya muku? Kafarki data fara rubewa waye ya biyamiki kudin asibiti aka cre? Bara dakikeyi waye yahani bara ya baki jari ke da 'ya'yanki? Amsr ita ce 'yar baba ita tamuku duk wnn.Allah ya yiwa 'yar baba albarka akwaita da tausayita danne duk. Abin da kukayi mata ta saka mukuda alheri. Yanzu katafaran asibiti tasa ana ginawa agarin babban mutum wa gareta a garin yanzu inbakuba? Ta ce min baba nasaa gina masalaci da mkrntr islamiya a babbanmutum za'a gina ajin yra'yan mata matasa da tsofaffi mata da maza sbdtsofaffi irin su iya abu su samu su koyi krtn salla.Asibiti kumada angama ginin zata zubamagunguna da gadajen kunciya kyauta sbdtalakwa. Hanne tsa shigabar kasa yasa a ginamuku titina ga ruwan fanfo da wutar lamtarki duk n bakuadalilinta, badan ita ba dawa zai tun da wani kauyewaishi babanmutum.Ynzu ta taimakeku a lkcn da kuke neman taimakobakamar ydda dukkaninku 'yan grin kukawulakanta ta kuka ki taimakonta a lkcn da take tsananin nemn taimakon ku. Bu ga amfanin bokoga,bokin dakike yadaw a gari, kina shela kinacewa yawan iskanci nake kai ta ba mkrnt ba, danabiye miki da tuni na cireta a bokon tazo ta zaunaagida ta zma kamar 'ya'yanki fa suka ki mkrnt gsunan babu wacce ka fi nunawa dg shigaban kasa sai ministan lfy hanna. Kullum gata ga shuganr ksa gamatarsa. Wani lkc har nusaiba kawarta tace matahnna wai ke ba zaki zauna ki huta ba , kullum kinakauye kina jigilar magani dkayn asibiti. Hanne tacemata hutu bai kamace ni ba nusaiba ta yayasunaneman taimako zcyta , jinin jikina da kuma dukiyata zanyi jihadi sbd Allah iyakar kokarin intaimakawa talakawa domib babu ciwon da yaficiwon talauci wahala.Allahu akbar,ina alfahari da hanna a matsayin 'yata,alummar musulmai suna alfaharida hanna amatsayinta na 'yar uwarsu musulma, 'yannigeria suna alfahari da hanna a amtsayinta na 'yarkasarsu, gwamnatin nigeria tana alfahari da hannaa matsayinta na minister lfy, 'yan niger suna alfaharida hanna a matsayinta na'yar uwarsu, jininsu sbdta gina asibiti a garin Dashi komai kyauta,taginamasallaci da mkrnt islamiya sunana nema sunan mkrntr ABUBAKAR IMAM ISILAMIYA.Yanxun a garin Dashi mace bata fargaba idanmijinta ya rasu ya barta da marayu tasan kotantamababu hanna ta tanadi mata tallafi mai tsoka.Babu abin da iya Abu da 'ya'aynta suke iya cewasai rike baki da girgiza kai suna jinjina wnndaukaka da hanna da mahaifinta. Iya abu ta langwabar da kai ta sharbe hawaye tacenayi kuskure ainun, gara da Allah yasa baka mutuba da ka mutu ina zan shiga da wnn tulin alhakinkadana dauka, ku yafe min.Ta fashe da kuka taci gaba cewa yanzu sai kadaure ka mayar dani dakina ni da 'ya'yana ka rungume mu zauna lfy da kishiyoyina su salmai.Salmai taimakeni kisa bakimlm ya mayar dani nasanki da tausayi kinga daman keki ka hada aurena damlm habu tun farko duk abida nayi miki abayakuskure ne yanzu zamu zauna lfy.Iya salmai ta zabura tace wacce ni? Abu kinfi karfina da dai da bansan halinki ba na jawoki jikinakika cuceni har hauka kika samun dole kka rabanida mijina abin kaunata, shekara 40 bana tare inatajin kaunarsa nayi sallama da aure sai yanxunAllah ya sake hadamu mukayi aure.Yanzu kina nufin in dauko shinkafar bera in zubawa kaina a abinci inci in mutu.Ya abu tasharbe hawaye tace yanzu salmai niceshinkafar berar? Mlm habu yayi murmushi yace abuai kinfi shinkafar bera tsiya saidai a kiraki da bombmai wargaza gari guda, to aini babu yadda za'ayi insake kara zamadake. Rabona da samun kwanciyar hnkl tun ranar dasalmai tasa na auro ki hakban huta ba sai ranr daaka dauke ni daga gidanki zuwa kabarina, tundaaga ranar nake hutawa a rayuwata har rana irinta yau.Kuma ina saka rana har karshen rywta zanci gaba da hutawa.Ina zan saake jajuboki da 'ya'yanki in hjajubawakaina tashin hnkl.Abu ta fashe da kuka , 'ya'yanta ma kuka sukesuna cewa baba yanxun gudunmu kake, yace haryanzu ku 'ya'yana ne kuma ba zan so ku tozarta ba ni ina suturce nayi alkawari zan dinga aikodirebana duk karshen wata yana kai muku kudi dakayan binci amma karku fiye zarga2 zuwa kanohar wani ya bata a hanya ku bari zan dinga yimuku aike.Iya abu ta sake kallon katafaran gidan nan tace babu inda zanje mlm sbd akwai igiyar aurena akanka tunda baka mutu ba.Mlm habu yace to tunda kina kokonto to bari natsnka igiyar kije na swake miki sbd bazan sakezama dake ba har abadaUwar biyu tanisa tace ikon Allah yau naga naci wai ba mlm hbun da kika raina bane? Kike zagi ta uwata uba yana kuka da idanuwansa mai yasa yanzukike sonsa?Mufa ba zamu zauna dake ba abu, yace ku tashikutafi zai ringa mukuaike.Suna zaune suna ta koke2 yarn suna fadin iya abu ke kika jawo mana ga rashin ilimi ga rashin tarbiyaduk biki bamu ba.Mlm habu ya shiga gida ya dauko buhunhunanabinci daga store suka zuba a wata doguwr motakirar bus yace direba ya kaisu babban mutum sukashiga suka tafi. Babu abinda suke sai kallon mlm habu ya zamawani danye shakaf dashi sai kace ba wnn yagulallntsohon nan bane, furfurr gemun nan buzu2 dukbabu an aske yasha farin danyan boyal a jikinsagawani farin gilashi a fuskarsa tsaddde hanna cetasa aka yankar masa a america data kaishi medical check up wanda zai kara masa gani tar,Babu wani ciwo da yake damunsa sai daimagungunn kara lfy da hanna take jubgo musutace suyi ta sha kamar bitamin A da bitamin E nasakwarin ido, karfin kashi da hana zubewar hakora.Lalla tsofaffin nan shar da su tubarkallah,KARSHE**** kusan kowanne weekend a americahanna keyi wajen mijinta, duk sati da aiki yayimaata yawa baza ta samu damar zuwa ba, haisamda yaran duka saisuzo suyi mata weekend danbasu da matsalar jirgi ko babu fasinja jirgi zai daukihannaa ya kaaita americaa. Kudi maasu gida rana sun aiki, lailla nn gaba zasusayi jirgin HAIRAMHANNA sbd zirga2 dagaa nigeriazuwa america.Wnn stin kaayataacciyar liyafa ambassado haisamya hada a america ta anabersary auransa daminister of health DR hanna haism abubukar da uwar gidnsa hj.ramlah haisam shitu.Mai girma shugaban kasan nig da uwar gidansa dadayawa daga kasoshin gwamnati , mahfa hanna,mahaifan haisam, mahaifan ramlah, iyalan gidanyaya habib, amratu da izzidin, kawu ahmada damatarsa hajir, rauda da mijinta hadddun 'yan uwa da abokan arziki duk an gayya cesu su hallaciwannan kayatacciyar liyafa da za'ayi a birinin USjirgi kawai zasu taka su haye kyauta ba tare daneman wata biza ba ko tikitin jirgi an riga anwankesu sbd mai girma shugabn kasa, hakashugaban kasar america Bush yasan da zuwansu. Haisam da hanna sun sami arzikin duniya fiye datnn mutum, duk da bayarwa suke amma tako inasamu suke.Sun mallaki gida a america, saudia, london ballekuma anan nig akwai wasu a abj, lagos, na kanoma baza su kirgu ba, babban mutum da wani a Dashi in take sauka idan taje.Duk wnn daula da hanna take ciki bata wulakantatalakawa taci abinci tare dasu tayi wasa da dariyadasu ta dauko abun duniya kuma ta basu.Hanna ta kara kyau data sami jin dadi kamr ahango jinin jikinta don fara fatarta, gata bata tsufa duk wanda yasanta shekaru 10 a baya idan yaganta yanzu haka zai ganta bata canja ba, sai kyaudata kara. Babu wanda zaiga 'ya'yanta yace ita tahaife su sbd 'yar karama da ita kamar yrny.Talakawan nig sun far yiwa kansu sha'awr haisamya tsaya takarar shugabanci kasarsu su zabe shi sun san zaiyi musu aiki. Ba talakawa kadai bashikansa mai girma shugaban kasr yana cewa haisamya shiryar da zarar ya sauka shi zai gaje shi, hakamanyan 'yan siyasr nig sun yarda da wnn btuu namai girma shugabn kasa.Kowacce safiyar duniyar nan haisam ji yake yana kara son hanna a ransa, itama kuma haka. Haisam,ramla, hanna da 'ya'yansu 5 suna zaune cikin jindadi da kwanciyar hnkl da kaunar juna. Arzikinsuyana ta bunkasa, basu ba ma duk wanda ya rabesuma yayi ban kwana da talauci balle 'yan uwansu najini balle uwa uba mahaifinsu. Mlm habu yayi ban kwana da talauci, kai uwar biyuynzu ta azurta 'yan uwanta da dama balle 'yarta tacikinta.Gidnsu ya zama gidan da kowa yake kawokukansa ake share musu. Mlm habu ya kanjebabban mutum amma wnn karon girmama shi kowa yake yi, gaisuwa har kasa ake zubewa ana yimasa.Iya abu ta dauwama cikin nadama duk sanda tagmlm habu is ta hau kuka tana rokonsa ya auretababu wanda take tsananin so sai shi, yakan bataamsa da cewa akai kasuwa bayaso. Allah sarki hanna bata manta da mkrnt ba sai tayihayar wani katafarn jirgi mai daukaar mutne daaribiyar, ta kawomin tikit guda dari biyar tace narabawa mkrnt masu matukar san zuwa america datsananin san ganinta suma tana gayyatar su wnnhadaddiyar liyafa da za'ayi.ALHAMDULILLAHIKARSHETAKU JAMILA UMAR TANKO (jut) TAREDA ANaM Dorayi whatsapp adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *