Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, April 3, 2017

haduwana da farida

adsense here HADUWANA DA FARIDA Karar shigowan sakon Whatsapp a wayata ne ya farkar dani daga baccin da ya fara daukata a kan keken dinkina. Kamar ba zan duba wayar ba, saboda idan da sabo na saba. kulli yaumin sakunan WhatsApp din basa rabo da zarya a wayata na mutane dabam- dabam a sassan kasar nan masu bibiyar labaraina a facebook...... Idan na ce biye musu zanyi, ba barina zasu yi neman abin sawa a bakina ba, shi yasa a duk lokacin da nake a shagon dinkin bana kula sakunan. Amma ga mamakina yau sai naji ina bukatar duba wayar in ga sakon waye ya shigo. Kamar kullum yau ma bakuwar lamba naci karo da ita da gajeren sakonta na sallama. Kamar ba zan amsa ba sai dai na daure na mayar da martanin sallamar. Wanda wanna shine farkon sanadin jefa kaina cikin wani mummunar hadari mtws dana sani keyace... Sakon lambar ya ci gaba da shigowa Yusuf Æbdullâhi Æ Jibagâ ko? Eh! Da wa nake magana? Na bada amsa tare da yin tawa tambayar. Farida, daya daga cikin fans dinka a Dandalin facebook, aka bani amsa, naga wani post da kayi kwanakin baya, naji dadin post din shi yasa nace bari nayi adding dinka nan in nuna maka jin dadina. Allah Sarki! Wane post kenan? Na sake tambayarta. Post din Hasashe game da matsalolin maza, gaskiya naji dadin post din sosai, ta bani amsa. Na gode, kuma da yardar Allah zan ci gaba da yin wasu post din wadanda suka fi wannan dadi. Allah ko? Gaskia ko yusuf idan ka ci gaba da nishandantar dani zan ji dadi sosai, saboda zaka sa in manta da bakin cikin da ke damuwata. Ke kuwa wane bakin ciki ne wannan? Na jefa mata tambaya cikin zakuwa da son jin damuwarta. Murmushi tayi gami da cewa kar ka damu idan lokaci yayi zaka sani. Ba zan iya tantance dogon lokacin da na dauka ina hira da baiwar Allar nan ba, abinda kawai na sani a ranar bata barni nayi dinki ba har lokacin barina shagon yayi. Tunda daga wannan lokacin shakuwa mai karfi ta kullu tsakaninmu da farida, duk yanda zanyi in samo labarin da zan tura mata wanda zai sakata nishadi sai nayi. Wani lokacin idan labaran suka kakare min sai naji kamar na koyi halin hankakar da wasu ke yi a duniyar fesbuk akan labaran mutane, sai kuma in tuna da yanda zuciyata ke tafasa a duk lokacin da naga wani ya satar min labari ya mayar da shi na sa, dole sai in fasa. Ranar da duk kuwa ban yi postin labari ba ko na tura mata a WhatsApp ba ranar zan sha kiran wayarta, a duk lokacin da ta kirani na kan samu karyar da nayi mata. A irin haka ne wata rana labaran suka kakare min, duk wata kafa da nake tunanin samun labari ta toshe na samu kusan kwana uku ba wani labari, sai ga kiran mutuniyar, bayan mun gaisa, ta fara aikinta wato tambayata a kan na daina nishadantar da ita, rasa karyar da zan yi mata nayi saboda ban son fada mata cewa labaran ne babu, karya nayi mata cewa bani da data ne a wayata Suscribtion dina ya kare. Har ga Allah na yi mata wannan karyar ne saboda bana tunani mace zata iya tura wa namiji kati babu wata alaka ta jini a tsakaninsu, amma ga mamakina bayan mun gama waya da ita kawai sai ga sakonta na tes ya shigo, ina dubawa lambobin kati na gani kasansu kuma tayi rubutu kamar haka:- yusuf ga kati nan kayi maleji dashi 1500 ne ba yawa. Ina gama karantawa kiranta nayi, tana dagawa nace Haba! Farida ya zaki min haka? Gaskiyi ki bar katinki bana so, ina da kudi zan saya da kaina. Nayi juyin duniyar nan akan ta barshi ta kiya, da taga na matsa sai cemin tayi sai dai idan ban so kar in loda in bai wa wani don ita ta riga ta bani kuma na raina kyautarta ne shi yasa na ce ba na so, kuma ta gode. Da naga ta hasala dole na dawo bata hakuri, da kyar ta sauko, sannan nayi mata godiya na kashe wayata. Ai kuwa tun daga ranar kati ya daina katsewa a wayata. Idan har bani da kudi a wayar a kalla ka sameni da naira dubu ciki, ba kuma ni nake saya da kaina ba ita ce da take turomin. DANA SANI KEYACE. Wannan dalilin jefa kaina cikin wahala na yanka kazan wahala ma kaina kumana fige naci karoda wani babban dutsen daya fasan zuciya asanadin farida.... Wannan fa..?ADUWANA DA FARIDA novels / HADUWANA DA FARIDA part 2 HADUWANA DA FARIDA part 2 Yau ma kamar kullum bayan mun gama gaisawa da farida a WhatsApp sai take cewa dani. In tambayeka mana. Ina jinki. kana da aure?. Na shafe kusan minti uku ina nazarin tambayar tata, ko zan gano dalilinta nayi min wannan tambayar amma ban gano ba, daga karshe dai na bata amsa tare da jefa mata tawa tambayar No i'm single, but why asking? ( A'a bani da aure, amma kuma me yasa kika tambayeni?) shiru ne ya ratsa tambayar tawa, har na tsawon minti goma, da dai naga shirun yayi yawa sai na sake tura mata wani sakon Hello! Farida kina kusa kuwa? Eh! Ta amsa min, Na rasa yanda zan baka amsar tambayarka ne. Saboda me? Na sake tambayarta Ina jin nauyin fitar maganar ne daga bakina, saboda ban san yanda zaka dauketa ba Tace dani. Feel free farida Just express your mind (kar ki ji komai kawai ki fadi abinda ke ranki). Ba zan boye maka komai ba... wutar soyayyarka ta dade tana ruruwa a zuciyata, har ta kai ga yi wa zuciyata mummunar illah, irin illar da in har baka bani daukin gaggawa ba, ko shakka babu tarwatsewa zata yi. Jin maganar tata nayi a wani bambarakwai, na jini duk wani wani iri, saboda wannan shi ne karo na farko a rayuwata da wata 'ya mace ta taba furta min kalmar SO, hasalima ni ko soyayya bana yi. Bakina da 'yan mata gaisawar mutumci. Shiru taga yayi yawa, ta kauda shirun da Hello! Ko maganata ta bata maka rai ne? In na bata maka rai kayi hakuri, nayi ta kokarin danne damuwata a zuciyata, na kasa ne shi yasa na fito fili na fada maka...... Ko daya farida baki batamin rai ba, hasalima farantamin rai kika yi, ai ko da wasa mutum yace yana sonka ya gama maka komai, ballanta kyakkyawa kamarki, kuma Babbar yarinya. In takaice muku zance. A ranar muka kulla yarjejeniyar Soyayya, muka aminta da zukatan Juna. ***** Tun daga ranar da muka kulla soyayya da farida, abin ya sauya salo, saboda a koda yaushe muna makale da juna, idan bama Chatting to waya muke. RASHIN SANI YAFI DARE DUHU... WATA SAFIYA..... Kamar kullum yau ma Chatting muke da Masoyiyar tawa sai musayar kalaman soyayya muke a tsakaninmu ta WhatsApp, sai nake cewa da ita. My dear kin san wani abu kuwa? No! my one sai ka fada. Idanuwa na sun kagauta suyi tozali da kyakkyawar surar nan taki, kunnuwana cike suke da daukin jin sautin muryarki kai tsaye ba wani shamaki a tsakaninmu, hancina ya kagauta da ya shanshani kamshim turaren jikin abar kaunata, yaushe ne mafarkin nan nawa zai zama gaskiya? Ka yi hakuri my one!, idan baka manta ba a ranar da muka fara haduwa na fada maka ina da wata damuwa har ka bukaci in fada maka damuwar nace ka bari in lokaci yayi zaka sani, yanzu lokacin da ya kamata in sanar da kai wannan damuwar. Hakika iyayena sun zabamin miji wanda ni kuma ba abinda na tsana a duniya kamarsa, shi yasa a duk lokacin da na tunashi sai inji gaba daya duniyar tayimin kunci, ba mai yayemin wannan kunci sai kai da labaranka, fahimtar da suka cewa na tsaneshi shi yasa suka sakamin tsatstsauran mataki na hani hulda da kowane irin namiji, ka kuwa ga yanzu haduwarmu da kai akwai matsala, amma na fara shawo kan iyayen nawa sun fara gano illar da ke tattare da auren dolen da suke so su yimin, sun fara yin sanyi, saboda haka ka kara hakuri da na ida shawo kansu, suka janye waccan maganar, to a lokacin sai ka gaji da ganina. My dear kenan, dama masoyi yana gajiya da ganin masoyiyarsa ne? Ina rokon Allah Ya nuna mana lokacin da matsalarmu zata yaye. Ameen cewarta. Na gama sakankancewa a zuciyata cewa nayi gamo da katar, kuma hakana yana gab da cimma ruwa, wai ashe da sauran rina a kaba. Kwana biyu da yin wannan maganar, ina shago bisa kekena ina dinki, wayata ta fara kururuwar neman agajina, ina dauko wayar kiran wata bakuwar lamba na gani. Nayi dana sanin daga kiran nan, Wallahi da na san za'a yimin wannan kiran da banyi fatan mallakar waya a rayuwata ba. WANNAN SHI NE BABBAN KUSKUREN DA NA TABA TAFKAWA A RAYUWATA. KU DAKACENI IN GAMA ZUBAR DA HAWAYEN NADAMA.A DA FARIDA novels / HADUWANA DA FARIDA part 3 HADUWANA DA FARIDA part 3 Posted by Bashir Sani Fesan on 20 Jan 2017 - 22:57 Daga wayar nayi tare da yin sallama, aka amsa daga daya bangaren. Samari kai ne saurayin farida ko? Aka tambayeni. Kafin amsa maka tambayarka, zan so sanin matsayinka ga faridar. Mahaifinta ne ni. Aka bani amsa sai bayan ya bani amsa, nayi nadamar yi masa tambayar, kayi Hakuri Abba ban san kai ne ba shi yasa, Ni ne masoyinta na bashi hakuri tare da amsa masa tambayarsa. Munyi magana da ita akan ta fitar da wanda zata aura tace kai ne zabinta shine na karbi lambarka a wajenta. Haka ne, na amsa masa ina so ne in ganka muyi magana saboda haka ka sameni gida gobe da sassafe. To! Abba sai dai ban san gidan ba. Ok bari zan turoma da adireshin gidan yanzu. Cike da farin ciki muka yi sallama da shi. Na dade ina jinjina al'amarin a cikin raina bayan na gama karanta adireshin gidan, wai dama ashe da diyar kwamandan soja nake soyayya ban sani ba. An ya ban kira ruwa ba kuwa? Na dade ina shawara da zuciyata, daya sashen zuciyata na cewa kar ka je Saif daya kuma na cewa kaje me zai faru idan kaje, don mahaifinta na soja ai ba zai dakeka baka yi masa laifin komai ba, daga karshe dai na yanke shawarar zanje komai ta fanjama fanjam. Wannan shi ne ganganci mafi girma da na taba aikatawa a rayuwata. Uhm waiyo rashin sani** Tun a lokacin nayi ta kokarin kiran layin farida amma yaki shiga, ina son fada mata wannan albishir ne duk da na san ta rigani sani, a WhatsApp ma sako uku ina tura mata ba reply. Daga karshe dai nace a raina wata kila caji ne babu a wayarta. WASHE GARI DA SAFE Gabana na faduwa na cusa kan babur dina cikin Barikin soja wannan shine karo na farko da na taba shiga barikin Sojoji na jaji dake KADUNA dukda yana garinmu ne. bayan tulin tambayoyin da na sha daga sojoji barkatai, aka sadani da gidan Kwamandan. Bayan na samawar wa babur dina matsugunni a kofar gidan, sai naje ga kofar na kwankwansa, wani mataccen Soja ya leko, ke ce bakon oga? Ya tambayeni da gurbatattar Hausarsa. Eh ni ne, na bashi amsa. Kai tsaye ya budemin kofa na shigo ya nunamin wata kujerar roba ya ce in zauna, zamana ke da wuya sai ga wasu samudawan sojoji guda biyu wadanda tunda nake a duniya ban taba gani sojoji kakkarfa kamar su ba, sai ji nayi sun rufeni da duka da wasu kulake, suka yi ta dukana har sai da suka sumar dani. Sanyin ruwan da aka zubamin shine yayi sanadiyar farfadowata daga suman da nayi wanda ba zan iya tantance iya adadin lokacin da na dauka a some ba, har yanzu dai Samudawan nan ne tsaye bisa kaina. Shegiya kwarton oga yau zaki ci ubanki, tashi kiyi sallen kwado suka umarceni da gurbatattar Hausarsu. Naga ta kaina ba irin nau'in azabar da basu ganamin ba a ranar, har sai da nayi dana sanin zuwana duniya, basu kyaleni ba sai da suka tabbatar bani da sauran mamora a tare dani sannan suka kwasheni kamar kayan wanki suka zube a wani matsakaicin daki wanda nake zaton na maigadi ne. Sai a lokacin nadama ta fara zomin, na tuna yanda mukayi da abokina AYS, ba yanda bai yi dani akan in kyale yarinyar nan ba, amma naki daga karshe ma da naga ya takuramin sai cewa nayi dashi yana bakin ciki ne dani don yaga na tsinci dami a kala. ko jiya sai da muka sha fama dashi yana kokarin hanani zuwa ni kuma nace sai na je sai yanzu na gano illar rashin bin shawara a lokacin fa ruwa ya kare wa dan kada bai gama wanka ba. Ina cikin wannan sake-saken najk an bude gambun dakin, kallo daya nayi masa na fahimci ko shi waye dogo ne mai faffadan kirji yana sanye da suit baka akwai sanko a kansa yana da tsawon fuska, shekarunsa zasu doshi sittin Kwamanda ne. Kayi kuskure dan samari neman matar soja, kuma a sojojin ma matar kwamanda. Duk da yanayin da nake ciki na azaba hakan bai hanani dago fuska na kalleshi cikin kaduwa ba ina mai jaddada girman maganar da ya fada a raina. WATA SABUWA... WAI DA MATAR AURE NAKE SOYAYYA ASHE. DA FARIDA novels / HADUWANA DA FARIDA part 4 HADUWANA DA FARIDA part 4 Posted by Bashir Sani Fesan on 20 Jan 2017 - 22:59 Kai tsaye kwamanda ya nemi kujera yazauna. ci gaba da maganarsa, ban yi tunanin zaka shigo hannuna da wuri haka ba, koda yake kuma ba abin mamaki ba ne domin kuwa Hausawa sun ce kuda wurin kwadayi ake mutuwa, to kai a kudan ma ka zarta kowa a kwadayi. Na rasa gano me ke damunku 'ya'yan talakawan nan ba zaku iya tsayawa a matsayinku ba ku nemi 'ya'yan talakawa tsaranku, sai kullum ku ne like da kyawawan mata, matan da aka yi don masu hannu da shuni in ban da wauta irin taku talakawae zai kai ku wurin. Ba sai na tambayeka ba dan samari ga mamaki nan karara a fuskarka, na san kana mamaki ne jin na ce maka farida matata ce, a farko kuma na ce maka 'yata ce ban maka karya ba dan samari a tarin shekaru na haifi farida, sai dai a zamantakewa ta aure matata ce, na san ba yanda za'a yi ta sanar da kai tana da aure ahi yasa nima na ce da kai ni ne mahaifinta saboda na san zaka fi saurin shigowa hannu, yanayin wahalar da nake ciki bai hanani gano dogon mutumin dake tsaye gabana mai wakiltar sunan kwamanda,,,, Allah yayi masa baiwar tarin surutu kamar waziri Aku ba. Ba tare da la'akari da me zan ce ba ya sake dorawa, babu abinda nake so a duniyar nan kamar matata farida, idan kuma akwai abinda na tsana a duniyar nan to abinda zai rabani da ita ne. gashi kai kana kokarin ka kwaceta daga gareni. Don girman Allah kayi hakuri, Wallahi ban san matarka ba ce, hasalima ban san tana da aure ba Wallahi da ko kusa ba zan nemeta ba. Na tari numfashinsa ina masa magiya. Murmushi Mugunta yayi min, sannan ya sake ci gaba da maganarsa kwantar da hankalinka ai na san baka san matata ba ce da ba zaka yi gangancin zuwa gidan nan ba domin rijiya ba wurin wasar makaho ba ne. Sai dai rashin sa'a daya kayi, ba na iya yafewa duk wanda ya rabi farida da sunan so, to kai gashi har soyayyar kuke yi. Lokaci daya kuma sai ya turbune fuska kamar wanda aka aikowa da sakon mutuwar faridar, sannan ya kira Samudawan nan da suka jibgeni dazu. Ku mikaminshi wurin M.P (Military Police) a yi masa horo mai tsanani har sai na waiwayeshi. Hankalina in yayi dubu a lokacin sai da ya tashi jin Kwamanda ya bada umarnin a kai ni wurin masu ladaftar da sojoji idan suka yi laifi wato Military Police, ihu na shiga yi ina masa magiya a kan yayi hakuri amma kamar baya jina. Wasa farin girki dukan da na sha a baya ba ko duka ba ne yanzu zan fara shan azaba Cakumata suka yi kamar tsumma suka yi waje, muna tafe ina sake- sake a raina ko shakka babu da za'a yi nadin sarkin wawaye to babu wanda ya dace a nada sai ni. Yaya daga haduwa da yarinya WhatsApp muna soyayya ban taba ganinta a zahiri ba haka ita ma bata taba ganina a zahiri ba sai dai a hoto, kawai wani ya kirani a waya wai mahaifinta ne yana son ganina sai kawai in tashi in tafi, in ma har da gaske ne ai ita ya kamata ta sanar dani sakon na mahaifinta ba wai shi ya kirani ba, a gefe daya kuma ina tunanin irin azabar da zan sha a hannun M.P. maganar wani abokina da ya taba zuwa tirenin din soja ta fadomin wai ko soja yayi laifi yana tsoron M.P su kamashi soboda azabar da zai sha a hannunsu. soja kenan, to ina ga ni farar hula, a farar hular ma zan fi dacewa da a kirani da mace mai tsohon ciki wata tara, a kan a kirani namiji saboda ragwancina. Da wadannan sake-saken muka isa suka hannuntani a hannunsu suka kama gabansu. Tashin hankali ba'a sa maka rana kwanana biyu cur a hannun M.P suna ganamim azaba har sai da na rika tunanin anya ba mutuwa ne nayi ba, a lahira ne nake shan wannan azabar, saboda kwata- kwata azabar bata yi kama da ta matambayan duniya ba. A washe garin kwana na uku kwamanda ya bada umarni a sakeni bayan ya gargadeni a kan ko mai sunan farida na kara kulawa na san sauran.. Satina uku cur a gida ina jinyar raunukan da M.P suka yimin ko kofar gida bana iya fita. ina kwance ina jinya na toshe duk wata kafa da nake ganin zan iya tuna farida nayi blocking dinta a facebook da WhatsApp, na goge lambobin wayarta da duk wasu hotuna da ta turomin nata. ina ganin mun yi bankwana kenan har abada, ashe wai da sauran rina a kaba . Bayan kamar wata daya da gama jinyata, ina zaune shago bisa keken dinkina na dukufa sai dinki nake wata madaidaiciyar mota launin ruwan siminti ta yada zango bakin kofar shagon dinkin, wani abokina ya taba fadamin sunan motar wai ko Continue Discussion ne sunanta. Irinta ne mijin kanwana hauwa.u jidda yake shiga Gabana ba karamar faduwa yayi ba lokacin da naga wata matashiyar budurwa ta fito daga motar kai tsaye ta kunno kai cikin shagon doguwa ce sai dai ba sosai ba tana da matsakaiciyar fuska mai dan tsawo dauke da dara-daran idanu da matsakaicin baki tana da saje a fuskarta launin fatarta kuwa wankan tarwada ce, shekarunta zasu iya kaiwa ashirin da uku zuwa da biyar, kallo daya nayi mata na shaidata kasancewar na saba ganin hotunanta. Farida ce. me kuma ta zo yi a shagona? tambayar da nayi wa kaina kenan...xakasanine..? Inka qara komawa chan..!♥ Home / HADUWANA DA FARIDA novels / HADUWANA DA FARIDA part 5 HADUWANA DA FARIDA part 5 Posted by Bashir Sani Fesan on 20 Jan 2017 - 23:01 Kamshin turaren da ya gauraye madaidacin shagon shi ya kara tabbatarmin da shigowarta ciki, gabana sai tsananta bugawa yake kara yi, tunanin masifar da zan sake shiga ya sani tsurewa. Sallamar da tayi min ce ta sa ba shiri na daidaita kaina nayi kokarin boye fargabar da ke kokarin bayyana a fuskata. Sannunka Tela, tace dani. Yauwa sannunki, na amsa mata. Dinki nake so kayimin, ta gabatarmin da bukatarta Ga shi kuwa kin zo a makare. Na fada cikin gatse. Murmushi tayi sannan tace wane irin makare sai kace wacce ta kawo dinki daren Sallah kuma tace yanzu take son a dinke mata. Ba wannan makarar kika yi ba Hajiya, ina nufin kin zo a lokacin da na daina yi wa mata dinki, na fadi haka ne saboda tsayuwarta cikin shagon ta fara gundirata kuma a koda yaushe gani nake Kwamanda zai iya fadowa cikin shagon. Maganar da na fada maimakon tayi sanadiyar barinta shagon, ga mamakina sai gani nayi ta nemi kujera ta zauna. Dan rainin hankali shi ne ka wani shareni kamar baka ganeni ba, to wurinka na zo magana nake so muyi, ta fada tana kokarin kakaro murmushi. A ina kuma kika san wannan sunan nawa? Na tambayeta Wane suna kake magana? Ta tambayeni ita ma. Dan rainin hankali mana. Na fada mata Dariya tayi har sai da kyawawan hakoranta suka bayyana. Au! Dama sunanka ne kenan? Kai dai ko yaushe baka rabo da abin dariya. Na gode amma zai fi kyau kiyimin bayanin ko ke wace ce? Na fada ina kokarin rufe babin wasar da take kokarin budewa. Na san ka san ko ni wace ce, amma tunda ka nuna baka sani ba zan kara sanar da kai, farida ce. Kona ce faridarka ce Ta sanar dani. Wace farida kenan? Na sake tambayarta. Haba my one kar ka mun haka please, yanzu ashe duk soyayyar da kake nunamin a waya yaudara ce ba sona kake yi ba? Ta fada cikin murya mai rauni. Look! Farida ba fa zan yarda ki sake jefani a wani bala'i ba, ba ni kadai ne saurayi a garin nan ba, zai fi kyau ki je ki nemi wani ki kara yaudararsa ni wacce kika yimin ta isa haka. Ka tsaya ka fahimceni yusuf ba wata yaudara tsakaninmu. Ta fada tana kokarin tabbatarmin da abinda ta fada har cikin zuciyarta ne. Dago fuskata nayi na kalli fuskarta ga mamakina hawaye na gani suna sartu a kan kyawawan kumatunta. Hawayen sun karayar dani amma sai na dake. Farida kenan, abinda baki fahimta ba shine an dade ana ruwa kasa na shanyewa. Kalamanki na yaudara ba zasu kara tasiri a gareni ba. Yanzu ke ko kunya ba zaki ji ba da aure a kanki ki rika bibiyar samari kina jaza musu fitina? Ka daure ka saurareni yusuf Wallahi gaskiya zan fada maka. Tace dani Ina jinki. Tasowa tayi daga inda take zaune tazo dab da telata, kusancin dake tsakaninmu har sai da na rika jin bugun numfashinta. Ka kalli kwayar idona ka fadamin idan ka ga yaudara a ciki. Ta bukaceni. Idan kin manta akwai bukatar na tunatar dake cewa ke matar aure ce fa, saboda haka kawai ki fadamin abinda kike son fadamin ina saurarenki. Kayi hakuri da masifar da na jefaka, da kuma boye makan da nayi cewa ni matar aure ce, ban yi haka don in cutar da kai ba, nayi ne saboda na san idan har na sanar da kai ni matar aure ce ba zaka kulani ba. Kuma ban san mijina ya dakeka ba sai daga baya, da ba yanda za'a yi na bari hakan ta faru, na san babu yanda za'a ka yarda da zancena idan har ban sanar da kai ko ni wace ce ba. Ina jinki.... Nace da ita saboda kalaman nata na yaudara sun fara isata. Kwamanda bai maka karya ba ni matarsa ce, amma ba na sonsa ba kuma da son raina na aureshi ba, iyayena ne suka auramin shi saboda la'akari da mukaminsa da kuma dukiyar da yake da ita, basu yi la'akari da cewar bana sonsa ba, kuma me zai je ya dawo bayan auren. Me yasa bakya sonsa? Na katseta da tambayata. Baka bukatar dogon bayani yusuf, ba sai na fada ba kai kanka kasan kyakkyawa kamata bata dace da tsoho mai tarin shekaru irin na Kwamanda ba. Na tsinci kaina a cikin kunci bayan tarewata a gidan Kwamanda, ba wai ya gaza wajen bani jin dadin duniya ba ne, ko daya, kawai dai na tsaneshi ne, wannan ne yasa ni fadawa a social network ko zan hadu da kawaye masu debemin kewa. Lokacin da na fara facebook shafukan bayar da dariya da saka nishadi nayi ta nema ina shigarsu, a garin lalubena ne na ci karo da kai wata kawa nane taban labarin indai labari nakeso na nemi Magana Jari nasha labari, Kuncin da nake fama da shi ya ragu, saboda labaran da nake karantawa a wadannan shafukan, sai dai duk cikin shafukan ba kamar naka domin kai gwanine. Kai DAN'ZAKI NE wane yaro Lokacin da na fara cin karo da lambarka ta WhatsApp ba karamin farin ciki nayi ba saboda naga hanya mafi sauki da zan rika samun labaranka. Yawan karanta labaranka da nake yi, sai naji ka fara birgeni, sannu a hankali sai naji na kamu da sonka. Ba karamar barazana na fuskanta ba Sabod a na san ba abu ne mai yiwuwa ba nayi soyayya da kai alhalin da aure a kaina,UWANA DA FARIDA novels / HADUWANA DA FARIDA part 6 HADUWANA DA FARIDA part 6 Posted by Bashir Sani Fesan on 20 Jan 2017 - 23:03 Farida taci gabada cewa, Ba karamar barazana na fuskanta ba Saboda na san ba abu ne mai yiwuwa ba nayi soyayya da kai alhalin da aure a kaina, Wannan ya sa na shiga tunanin mafita, daga baya na yanke shawarar na boye maka ina da aure. Idan har ba yaudarata kike yi ba maganar da kika fada gaskiya ne ya akayi Kwamanda ya san muna tare? Akasi aka samu nayi rashin lafiya ne mai tsanani wacce ta kaini ga kwanciya asibiti, bana raba daya biyu WhatsApp dina ya shiga yai min bincike anan yaga Chat dina da kai, kuma har kaje gidan ka dawo ban san an yi ba ina Asibiti. To ya aka yi kika sani? Bayan kin ce ba ki gidan. Shi ne ya sanar dani bayan naji sauki. To wane mataki ya dauka a kanki? Hmm! Yusuf kenan, idan akwai abinda Kwamanda ya tsana a rayuwarsa to bacin raina ne, shi yasa duk abinda nayi bayamin fada bare har ya dau wani mataki a kaina. To yanzu me kika zo yi wurina? Kuma me kike so in yi maki? Hakuri na zo baka, a kan abinda yai maka, sannan kuma naga kayi blocking dina a facebook da WhatsApp shi ne na so jin dalilin hakan? Zancen Hakuri nayi, zancen Blocking kuma saboda ba zai yiwu in ci gaba da soyyaya da matar aure ba, a matan auren ma kuma matar soja. Sojan ma kwamanda Ba soyayya zamu ci gaba da yi ba yusuf, kawai gaisawa zamu rika yi kuma ka ci gaba da turomin Labarai. Ta fada tana yi min wani kallo, wanda ni a ganina na yaudara ne. Ba zai yiwu ba farida, zai fi kyau ki kama gabanki kar ki sake jefani a wata musibar. Ka gasgatani yusuf nayi maka Alkawarin babu abinda zai sameka wancan karon ma akasi aka samu. Tace dani Na fada maki fa ba zai yiwu ba, ki sani ko wannan hirar da muke yanzu zunubi ne muke kwasa saboda haka kawai ki kyaleni kar ki sani fadawa cikin fushin ubangiji. Ba irin magiyar da bata yi ba, amma naki amincewa, dole ta hakura. Da zata tafi kudi ta dauko daga jakarta wadanda ba xan iya cewa ga adadinsu ba, amma a kiyasin da nayi kudade ne masu tarin yawa ta ajiye a kan telata, Na meye? Na tambayeta. Baka nayi, na san ba zaka rasa 'yan hidindimu a gabanka ba. Tace dani tana kokarin fita. Kuma sai na ce dake bani da kudin da zan yi hidindimun nawa ko? Kar ki mayar dani wata haja mana, wacce zaki rika saye da kudi a duk lokacin da kika ga dama. Na fada a fusace. Kayi hakuri ba nufi na ba kenan, gani nayi ba komai ba ne don na baka kyauta, amma tunda kayi min wata fassara, shi kenan ba zan kara ba. Zai fi kyau hakan, nace da ita ina kokarin mika mata kudin. Na dauka ta hakura kamar yanda ta nuna ashe tana kasa tana dabo, gwara ma a ce na amince da bukatarta a kan abinda ya biyo baya HAKAN SHINE BABBAN KUSKURENA DAYAFI NABAYA.. Hankalina ba karamar kwanciya yayi ba ganin cewa na yadda kwallon manguro zan huta da kuda. Bayan kamar kwana biyar da zuwan farida shagon da nake dinki. Da sassafe ina kwance dakina dake kofar gidanmu na ji kanina Hafizu yana kwankwasamin kofa, koda na bude yake shaidamin wai nayi bakuwa tana nan kofar gida tana jira. Kaina ba karamar daurewa yayi ba jin cewa wata ta zo nemana har gida domin kuwa wannan shi ne karo na farko da mace ta taba zuwa nemana a gida. Duk matan da nake yi wa dinki sai dai su zo nemana a shago kuma ko basu sameni ba Aminu wanda muke dinki tare zai kirani a waya in zo. Cike da mamaki na fito daga dakin na nufi kofar gidanmu, tun daga nesa na hango mota tsugunne a kofar gidan, bana raba daya biyu motar farida'ce gabana ya bada rass! Kamar in juya sai dai na daure na isa. Ta bude kofar sashen mai tuki ta zuro kafafunta waje sanye cikin jan material rike da waya kirar Sony Ericson Xperia tana chating. Farida ce. Murmushi ta jefeni da shi yayin da ni kuma na daure fuska tare da jeho mata tambaya. Me kika zo yi a gidanmu? Wurinka na zo yusuf ta fada tana kokarin mikewa tsaye. Haba! Farida yanzu kina ganin ya dace a matsayinki na matar aure ki rika zuwa wajena, kuma baki tunanin zuwanki gidanmu zai iya haifarmin da matsala wajen iyayena? kuma kin san mijinki yai min tsakani da ke. Na ce da ita, cikin muryar rarrashi saboda gaba daya na gama tsinkewa da al'amarinta.ADUWANA DA FARIDA novels / HADUWANA DA FARIDA part 7 HADUWANA DA FARIDA part 7 Posted by Bashir Sani Fesan on 21 Jan 2017 - 17:18 Na ce da ita, cikin muryar rarrashi saboda gaba daya na gama tsinkewa da al'amarinta. Laifinka ne Darling saboda na fada maka ba zan iya rayuwa ba kai ba, na bukaci ka bari mu ci gaba da waya kuma mu dinga communicating a social network kamar da amma ka ki, na yi iya kokarina in ga cewar na fitar da kai cikin raina abu ya faskara. Ta fada tana yi min fari da idanunta. Amma kuma ai ya kamata ki san cewa cikin fushin ubangiji ne kike son jefani, ta yaya zan amince da wannan bukatar taki, kuma idan ma ban ji tsoron Allah ba ai ko don gudun azabar mijinki dole in kaurace maki. Na ce da ita Calm down mana yusuf in dai matsalar mijina ce nayi maka alkawarin ba zai koma tabamin kai ba. Tayi saurin katseni.... Wasa-wasa farida ta maida unguwarmu kamar gidansu kusan kullum sai ta zo wajena in bata zo gidanmu ba to zata sameni shago kuma kullum ta zo zancen daya ne, ba irin magiyar da ban yi mata ba akan ta daina zuwa wajena, sai cewa tayi idan ina so ta daina zuwa inda nake to in bari mu ci gaba da hulda a social network kamar yanda muke a da, tun abin baya damuna har ya fara damuna ga mutanen unguwarmu sun fara tsegumina,gidanmu kuwa mahaifiyata kullum sai tayi min fada akan yawan zuwan da farida ke yi nemana tun inai mata karyar dinki ne ke kawota har ta daina yarda da karyar. Da na fahimci ba zata daina zuwa ba tilas na amince da bukatar.... BABBAN GANGANCINA KENAN DANAYI ARAYUWA. Amincewar da nayi wa farida muka ci gaba da hulda a social network da kuma ta waya kamar da, ya sa ta daina zuwa unguwarmu. Ko da yaushe sai dai mu rika haduwa a facebook, ko WhatsApp, ko kuma ta kirani a waya. Haka Al'amarin ya ci gaba da kasancewa har zuwa wasu 'yan kwanaki... Yau ma kamar kullum zaune nake a kan keken dinkina, ina dinki. Kamar daga sama nagansu, sun fado cikin shagon, basu tsaya cewa dani komai ba cakumoni kawai suka yi suka yi waje dani suka yi jifa dani cikin motarsu kirar Hilux, kamar fitar kibiya daga kwari, haka suka figi motar suka yi gaba dani. Yaran Kwamanda ne (Sojoji) Tun cikin motar suka fara nukurkusata, koda muka isa barikin tuni na fice daga hayyacina. Koda hankalina ya dawo jikina, na ganni ne a wani daki da zan iya kira da kurkuku mafi kunci a duniya. Ba sai na tsaya wani bincike ba na san Kwamanda ne ya sa aka kamoni saboda kunnen uwar shegu da nayi da gargadinsa. Nadama ce ta zomin irin wacce ban taba yinta a rayuwata ba tunanin wahalar da na sha kwanakin baya a hannunsa ta ya zomin, lokaci daya kuma tsanar farida ta shigeni lokacin da na tuna da alkawarin da ta yi min a farkon zuwanta shagon dinkina. Tabbas farida annoba ce a rayuwata... Karar bude dakin ce ta katseni daga tunanin da nake yi lokaci daya tsoro ya dabaibayeni na tsura wa kofar idanu, don ganin wa zai shigo. Kwamanda ne ya shigo. Sanye yake cikin kaki (Uniform) ba kamar wancan karon ba, kallo daya nayi wa fuskarsa na fahimci ransa yayi mutukar baci. Kunnen kashi ne da kai ko yaro? Ya jefamin tambaya. Bai bani damar amsa masa tambayarsa ba kai tsaye ya ci gaba da magana. Ko da yake laifina ne da na baka damar da zaka bijirewa umarnina, da na batar da kai tun a wancan lokacin da tuni nayi maganin taurin kan nan naka. Amma ko yanzu ban makara ba, ina da damar yin hakan. Ban ankara ba sai ganinsa nayi rike da bindiga yana kokarin saita kokon kaina. Saboda firgici ban san lokacin da fitsari ya kubucemin a wando ba,..nan danan nahau addu'an daduk tafadomin abakina..tsawon minti 3 nadauka inajiran inji saukan bindigar akaina amma shiruUWANA DA FARIDA novels / HADUWANA DA FARIDA part 8 the end HADUWANA DA FARIDA part 8 the end Posted by Bashir Sani Fesan on 21 Jan 2017 - 17:21 nan danan nahau addu'an daduk tafadomin abakina..tsawon minti 3 nadauka inajiran inji saukan bindigar akaina amma shiru karshen labarin na rufe idanuna ina jiran saukar harsashe a kokonkaina. Na share akalla mintina uku ina jiran saukar harsashi a kokon kaina. Shirun da na ji ce ta sani bude idanuna. Ganinsa nayi ya ajiye bindigar ya samu wuri ya zauna sai faman huci yake kamar wata kasa. Ko me ya hanashi harbe kokon kan nawa? Kamar yanda yayi ikirari. Kamar ya san amsar da nake bukata, sai kawai ya fara amsamin. Kaci sa'a, ko kuma in ce Allah Ya yi lokacin mutuwar bai yi ba, shi yasa naji tausayinka. Wannan shi ne karo na farko da na saita bindigata akan wani mutun, da nufin harbinsa, kuma ban harbeshi ba. Saboda haka yanzu zan maka Adalci daya. Wancan karon na yi maka hukunci da laifin GANGANCI, alhalin baka yi GANGANCIN ba. TSAUTSAYI ne yasa ka yin laifin, yanzu kuma kayi min GANGANCI, hukuncin ganganci ne ya kamata in zartar a kanka, amma ba zan yi hakan ba, zan yi maka rangwame, in yima hukunci da wancan laifinka na TSAUTSAYI. Zan karya hannuwan nan naka biyu, wadanda kake amfani da su kana chatin da matan mutane. Sojoji biyu ya kira daga waje ya basu umurnin karya hannuwa duka biyun sannan ya ficewarsa. Ina ji, ina gani suka rika kokowa da hunnuwana kamar masu kokowa da icce har sai da suka kakkaryani, saboda zafin ciwo ban san lokacin da na some ba. Lokacin da na farka, cikin shagon dinkina na ganni mutane sun kewayeni, bayan sun tambayeni inda ke min ciwo nayi musu bayani wuraren da na karye. Suka kwasheni sai wurin mai dori aka doramin hannuwan nawa sannan suka dawo dani gida domin jinya.. yadda kuka Nayi zaton tunda kwamanda yasa anmun hukunci na karshe shikenan na huta. Ashe akwai abunda yafi hukuncin kwamanda zafi. Kaikanka me karatu dakasha mamakin abunda nagani. Zuciyana ta kone hanjin cikina yakada domin abunda kunnuwa suke jiyemun nayi kukan nadama awannar ranar. Nakwana da mamakin halin mata. Ashe dama haka mace take da sharri? Nida abokaina 'yan,uwana munsha mamakin abunda muka gani. Barida nabaku labarin kawai GAYADDA ABUN YAKASANCE Washe gari ina kwance cikin gidanmu, abokina waziri aku ya zo dubina, muna hira. Gefena kuma 'yar autar dakinmu ne. Hauwa'u jidda. Tayimun kirki sosai na kayan cikin saniya. Zaune take tana zubar da hawaye domin tausayin datake gwadawa akaina kasancewar itane kaf dakinmu allah ya hada jinana danata. Samada sauran 'yan.uwana sai ga sakon farida ya shigo wayata na ce da waziri aku ya karantamin sakon kasancewar bani da hannuwan rike wayar bare ina karantashi da kaina. Ga sakon kamar haka.. "Gareki Wawiyar zuciya mai cike da kwadayi, ka bani mamaki Hussaini domin kuwa ban zaci zan yi nasara a wannan wasan da sauki haka ba. Na zaci wasan zai yimin wahala ganin cewar da gwani ne zan yi wasar, sai gashi na sami akasin hakan, ashe hangen kitse ne nake yi wa rogo, a yanda nake ganin rubuce-rubucenka na dauka kai gwani ne a wannan wasan ashe wai baka ma san yanda a ke buga wasan ba. Na san zaka bukaci sanin dalilin buga wasan, to zahirin gaskia lokacin da na fara karo da labaranka, haka kawai na ji na tsaneka, na dade ina nazarin dalilin da yasa na tsaneka, sai daga baya na fahimci ba komai ne ya sa ni tsanarka ba sai ganin cewa kai ba wani marubuci ba, amma ka dage, wai kai sai kayi rubutu kuma wani abin karin haushi duk rubuce-rubucenka su kan kare ne a wance ta yaudareka, wance ta ci amanarka, wance kuma tayi maka wulakanci, zancen duk daya ne. Shi yasa na ga ya kamata idan duk wadancan da kake fada sharri ne kake musu, to ni bari in yi maka na gaskiya sai kayi mai dalili Da nayi niyyar kyaleka a dukan farko da mijina yai maka sai kuma naga ai baka doku ba tunda gashi baka daina abinda kake yi a da ba, don haka sai na ga wancan wasan first half ne muka buga ya kamata a ce mun buga second half. Yanzu kam wasa ya kare tunda nayi nasara. Kar ka manta da ni domin kuwa nima ba zan manta da kai ba. Hawayene ke zuba idon domin jin wannan mummunar sakon na farida nasha mamaki nayi zaton sone na gaskiya ashe cutane dama Tabbas wannan mata ta kai Azzaluma nq fada a raina Bata yi kuskure ba da ta kira zuciyata da wawiyar zuciya kuma mai kwadayi, domin kuwa su ne suka bata damar yin nasara a wannan basajar da tayi min wacce ta kira da wasa, sai dai tayi kuskure da ta ce ban san yanda a ke buga wasan ba, domin kuwa ni malamin wannan wasar ne kawai dai idanuna sun rufe saboda kwadayi da kuma wauta, shi yasa na kasa gano bakin zareb wasar, ga shi garin kwadayin nawa na rasa hannuwan da nake rubutun da su, kuma nake dinki ina neman abin sakawa a bakin salati. Karyata ta kare.... Shi yasa da na samu sauki naga ya kamata in zo wa duniyar facebook da wannan labari ko 'yan uwana samari zasu tsira daga tarkon Basajar matan social network. . KARSHE WANNAN SHINE KARSHEN LABARIN adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *