Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, April 3, 2017

HAKA NAKE SANKI complete

adsense here Haka Nake Sanki Written by Fatima Aminu Ya'u F.A.Ya'u Sauri kawai take kanta akasa dan bata san magariba tai mata juyawar daxatai sukai ido biyu da shi nan taji gabanta ya fadi ayan kwanakin nan tafuskanci kullum setaga wannan mutumin tun bata fara xargin ita yake bi ba harta fuskanta nan take bugun xuciyarta ya karu wani tsoro ya xiyarci xuciyarta sakamakon magari ba tayi ita daya ke tafe seshi dake binta a baya nan ta kara saurinta. Dasaurinta ta shiga gidan ko sallama batai ba dan yadda taga shima mutumin saurin yake daga bisani ta nemeshi ta rasa haba mesunan manya yaxaki shigo gida ba sallama umma karene ya biyoni kinsan in yanma tayi aikam naga alama toma me kika tsaya yi a hanya se yanxu xaki dawo wallahi malan muktar ne ya tsaidamu yadanmana nasiha to yayi kyau maxa cire kayan kixo ki kaima hajiya karima tuwonnan to umma ta shige daki dan aje jakarta bayan ta shafa doguwar addu'ar tata tafito umma ina tuwon gashinan na samirane ki gaisheta seda taxo xaure ta tuna dashi aikuwa nan gabanta ya soma faduwa kamar yadda ta xata yana kofar gidan azaune bata nuna alamar taganshiba tai gurin da"aka aikeran tai sa'a kuwa me gadi na kusa ya bude tashige. Bayan sun dan taba hira Aisha ta rakota xuwa kofar gida vayanan ta fada aranta tadanji dadi sukai sallama ta shiga gida. Shi kansa yarasa me kedamunsa yabi ya rikice yabi ya manta da duk abinda yake ciki yarasa me yasa yake biyema xuciyarsa indai begantaba baya jin dadi duk irin korafin da ake masa a gida da gun aiki yashanye akullum ya tunkareta se yaga tanai masa wani kwarjini xuciyar sa na fada masa yadaure anman ya kasa. Tafe take cikin nishadi dan yau kam bataga mayenba koma nace aljanin yadda tasama ranta kenan gani harta kawo titi bata ganshi ba yasa ta yadda aljanine addu'arta ta koreshi sedai me wata dalleliyar mota ta tsaya gabanta ya xuge glass din shine tagani yana sakar mata murmushi tai saurin matsawa ya fito kadija ina kwana ya fadi gavanta ya cigaba da faduwa au yama san sunana bata jira ko bashi amsaba ta shige dansahun da ta tsaida. Waike bakyajin mutanene taji muryar me dansahun yi hakuri vanjika ba ta sauko gami da mika masa kudinsa tunanin abinda ta aikata take mesa bara tsaya ta amsa gaisuwarba aida tsaya watakilma taji shi waye tarokeshi ya kyaleta harra shiga aji tana saka da war wara. Yau sati na biyu kenan bata ganshi a hanyaba tun bata damuwa har tadamu yakai duk inda tasan tana ganinsa tana bi bashi va dalilinsa wani xubinma har fita take tadan yawata ko xata ganshi abinda yake ba halinta bane tarasa me yasa ta damu dashi haka duda xuciyarta na fada mata kawai tanason ta ganshine ta bashi hakuri vata da wani abin tunawa akoda yaushe banda fuskarsa cikin sanyin safiyarnan yana mata murmushi muryarsa akullum amsakuwa take matq khadija ina kwana. Kwance take tana kallon fankar dakin maganar vilkisu take tubawa khadija ko kiyarda ko karki yarda u are in love taurin ran xuciyarki yaki yarda wani hawaye suka xubo mata a hankula ta furta nayadda dake wallahi am in love but with whom bansanshi ba nida nai alkawarin baxan tava soyayyaba yaxanyi toma inshi din va sona yakeba xuciyarta tabata amsa tabvas va sanki yake ba yau tsahin kwanaki benemekiba bema tava cewafa yana sankiba toma inyace yanasanki kekinsan ke ko wace tafashe da kuka tunowa datai itadin wace da tunoshi cikin rantsattsiyar motarsa tasan ba kowanne irin iyayene xasu yarda sansu ya aureta ba. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Hawayenta ya karu ga wani kunci da ya xiyarce ta ko mai ta tuna oho tai murmushi gami da goge hawayen a hankula tace Allah kaine abin godiya gami da mikewa ta dauro alwala dan bayyanama Allah bukatunta. Washe gari da sassafe ta kintsa bayan ta gama aikin gida bata ko tsaya bi takan karyawa ba taima umma sallama ta wuce makaranta tai sa'ar shiga sch din da wuri dan haka ya hau aikinta matsayinta na mai dan kwali. Ko ayauma tasanya ran ganinsa duda tayadda duk abinda tasa aranta be cika xama gaskiya ba duk yadda umaima tai taxo su tafi taki dan ita yau aka tai niyar tafiya ko Allah xaisa taganshi tarasa wacce irin xuciya gareta namiji xai xo da'alamar so tunkan ya furta xata koreshi inya tafi taji duniya shi take san gani daga bisani ta mance sedai fame shi wannan nasa yafi na kowa domin tarasa meyasa har yau takasa mancewa dashi. Nasir ne xaune gaban gadon yai tagumi abu buwa duk sunbi sun cushe masa gashi mamarsa ba lpy gashi yanasan ganin khadijansa yarinyar data xama wani bari na jikinsa yarinyarda baya minti biyu cikakke se ya tuna ta yasani ita tama mance dashi watakil ma murna take ta dena ganinsa dan ya fuskanci ba tun yau ba bata san ganinsa. Nasair nasir yaji muryar maman tasa asanyaye ya mike xuwa inda take kaga nadan samu sauki gara kaxo katafi aikinka karsumaka wani abu yai dan murmushin karfin hali ai bakomai abinda nine director anman ai gunka nakasa xasu dauka eh hakane mama anman kibari kisake warwarewa tukunna to shikensn Allah ma albarka ya amsa amin mamata. Yau kam jikin mamar da sauki dan haka ya yanke shawarar yau da yardar Allah xe gabatar ma da khadija kansa xai cire duk wani abu na tsoro tsoro da gwarjuninta dan hakane ma gaba daya kayan war dropped dinsa ya futo dasu ya xabi wannan yace beba yaxabi wancan secan idonsa yakai kan shadda sky blue me dinki kalarta tai masifar kyau. Kimanin karfe hudu yafito tsaf dashi yai kyau sosai kai kace sabon angone koda ummansa ta ganshi tai murmushi dan albarka ina xuwa haka xani gidansu najib ne tai dariya to ka gaisheta yadan jiyo yakalleta kunya ta kamashi se nadawo to se kadawa ya fita yana dariya yanasan ummansa musanman yadda take gane duk wani hali da yake ciki koda kuwa ya boye mata. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Hudu da rabi tai masa kofar gidansu dan yasan yau bata islamiyya yafi mintina goma be samu dan aikeba yarasa yadda xaiyi can ya hango wani yaro xai shiga gidansu Aisha yai kwala masa kira yaron haryai kamar yaki xuwa se kuma ya yaxo yawwa dan albarka shiga gidannan ka kiramun khadija to yace gami da shiga. Wai khadija taxo maxa jeka kace batanan tafadi da sauri xatonta umma batajiba harya kai xaure umma ta kwala masa kira Abdallah jeka kace tana xuwa yafice waike me sunan manya yaushe ne xaki dai na abinda kike nafara gajiya da halinki ko cemiki akai ahaka xaki dawwama tai narai narai da ido anman umma yimun shuru inkuma ban isa insaki bane seki fadan ta mike gami da xura hijabinta tai kofar gida. Tsaye yake jikin motarsa sanye da gilas fari yai masa kyau sosai ga sajen fuskarsa ya kwanta luf kallo daya tai masa wani kwarjinsa ya karu kan fuskarsa tadauke idonta. Ahankula tai masa sallama batama tsammanin yajita ga mamakinta taji ya amsa barka da rana ta fadi ayayinda bata sanma ta fadi ba duk xuciyarta a rikice take karfun hali kawai tai ta daure bata nuna ba duda tana xaton ya fuskanta. Koda shike shidin farin shigane duk ya rasa mai xai ce mata duda tun jiya yake practice tadan dago batare da tabari sun hada ido ba tace ko xamu matsa kan tuduncan ba damuwa. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Sun xauna nadan wani lokaci kowa da abinda yake sakawa cikin ransa kafin Nasir ya jarumtar katse musu shurun da fadin khadija ta dago ta kalleshi na'am nasan xaki mamakin ganina tai murmushi ai ban mamakiba yadan kalleta sabida tace bakomai Allah da komai ya fada taidan murmushi gami da yin shiru any way sunana Nasir muhammad Abdulmalik ina aiki a asibitina fa'ams special hospital batun yauba ina ganinki inasan namiki magana sedai bansan ciki kula yarinya kan hanya ba. Tai murmushi naji sedai gaskiya ban fuskanci abinda kake nufi ba ta fadi dan jin mexai ce yai murmushi haba dja nasan kin fuskanta inba damuwa ni bansan ciki doguwar soyayya awaje ya kike gani tadan kalleshi kamar ya fa ina nufin xan turo iyayena ai mgn lallaifa ta fadi cikin ranta wannan kaine sarkin sauri hango wata shekarar banda abinsa daga haduwa yau kowata mgnr kirki vasuyi ba sai maganar aure tai dariya kadai bari mu fuskanci juna tukunna yai murmushi dan yafuskanci ko bakomai yasamu shiga. Ledodin da ya sayo nata gift ya dauko mata gashi naxan wuce mene tace inkinje kya gani nidai baxan karba ba dan Allah karki mun haka Wallahi baxan karba ba sabida me kawai to shikenan naji ban no dinki ai banda waya pls karmuyi haka dake.pls kiban wallahi banda waya to naji yaushe xan dawo duk sanda ka shirya ohhhhp ya fadi haba dja. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Tai dan murmushi ya nasir kenan yaji dadin rike sunansa datai bakiji ba ta kalleshi nixan wuce anman wata alfarma xaki mun kice mun wani abu mana da xan dinga tunawa dake kafin nadawo toshikenan kagaida gida ah bakamar wannan ba tai dariya to kamar me kamar i love u ta rufe fuska gami da shigewa gida tana murmushu shima yadan murmusa kafun ya mike yabar wajen. Koda ta koma gida umma naxaune a tsakar gida tadan kalli khadija yakika dade uhum umma daman daman tashigewarta daki umman tai murmushi kawai burinta yau taga auren khadijarta. Yaukam nasir rageggen bacci yai dan cikin farin ciki yake duk yakasa sukuni ba abinda yaxamar masa abaun tunawa sai firarsu da khadija. Kafin wani lokaci shakuwa mai xafi da so da kauna ta shiga tsakanin khadija da nasir har basa iya boyewa duk kasan tuwar nasir miskili anman gurin khadija akune. Ayanxu ba'abinda ke damun khadija cikin soyayayyarsu sai inta tuna da asalinta ta tuna da ita din wace tasani komai daren dadewa sai nasir yaji koya xai karbi lamarin ko watakil ma ya tsaneta ko iyayensa xasu yarda ya aureta. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Yau tunda ta tashi take jinta wani irin kamar ma kartaje makarantar dan batasan karya record dinta na rashin fashiba da ba inda xaka haka ta daure ta tafi. Ko a sch dinma bata wani tabuka abin kirkiba kawai jinsu take yayin da bilkisu kawarta ta takura mata wai sai ta fada mata wanda take so taje ta fada masa sanin halin bilkin natsokana yasa har yau takasa fada mata game da nasir duda kuwa bata da kamarta. Gaba daya ajin ya rikice surutu kawai kake ji na yan ajin kowanne group kakalla da abinda ke damunsu da abinda suke tattaunawa da alama sunajin dadin rashin shigowar malamin nasu suma yan group dinsu khadija suna hirar da suka saba wato hirar irin labarun da'ake karantawa jokes gaba dayansu cikin nishadi suke inka dauke khadija dabama tasan me sukeba binsu kawai take da ido maryan tadan kalli Fatima wai meke damun kadija ne wayasan mata yan miskikancinne ya motsa inji Aisha haba bawani aiduda jama'a nacewa itadin shuru shuruce munsan karyane tunda kuwa har damunmu take kawai dai da abinda ke damunta Fatima ta fada ku dalla ku kyaleta ninasan me ke damunta bilki ta fada Aisha ta xuro kunne shi yasa nake sanki kawalli guntsa mana anawa ta miko hannu to lashe money kedai kudi kudi tonaji xakumun note eh munji she is in love gaba daya suka hada baki da karfi gami da gwalo ido😳 what love gaba daya idon ajin yadawo kansu inda yai dai dai da dawowar khadija daga tunani suka saka dariya gami da tafawa what a surprise Fatima ta fada tavdi daman anfada ai masu cika baki kan love is nothing basu iya kamuwaba tai dariya wallahi ku yan iskane shikenan mutun baida damuwa seta love banajin dadi ne kunsan wani xubin inna tuna da matsayina gaba daya suka nutsu dan basa san take tunawa da wannan batun kowacce ta hau mata nasiha. Tana san kawayen nata domin sudin bata da kamarsu basa taba nuna mata tsangwama ko banbanci face ma duk wata matsala fabata fi karfinsuba suke shige mata faba xamowarsu tare tasamu yanci gameda abinda sauran dalibai ke mata tai dariya gami da rungume su shi yasa nake sanku naji yanxu kaina ke ciwo bari na kwanta kafin atashi mudai bamu yardava ki tashi muyi fira Allah kaina ke ciwo ainai muku alkawarin ayau vaxan kuma damuwaba to shikenan bari nakarbo miki mgni inji bilki kema kinsan bansan maganin sch dinnan Aisha tace inada bari akawo ruwa seki sha nifa magninne bana so innadanyi baccin xai sauka to shikenan kowanne malamine yaxo kuce bani da lpy. Da murmushinta kan fuskarta daga gani tana cikin farin cikin ganinsa ina ya na barka da yanma bai amsaba abinda bata sava ganiba fuskarsa adaure yana ko naima lefine lefi lefi fa kika ce aini abinda kika mun yafi karfin lefi wallahi khadija kin ban mamaki yanxu ace atsakaninmu akwai yaudara da cin amana da ha inci kinban mamaki ban taba xaton kedin munafika bace se yau nasir me nayi ban cancanci wadannan miyagun sunayenba aikin cancanci fiye da haka naji kafadan menai na kare kaina kare kankifa kika ce uhum yawani saki murmushi daga gani na takaici ne kin cuceni khadija dakika sa nai xurfi asanki alhalin kinsan bamu dace ba anfadamin ko ke wace inaso kimun wata alfarma ki mance da kinsanni kamar yadda na shafeki a babina amma anman what ya fada cikin daga murya gami da cewa baki da abinda xaki cemun cutace kin cuce ni ya shige motarsa tai saurin rike mirfir dan Allah katsaya kasaurareni kisakar min mota ko wallahi yanxu nai hajijiya dake dan Allah kasaurareni xaki saki kosaina makeki yako hankadata gami da jan motarsa ya badeta da kura ta durkushe a gurin tana kuka. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Haba khadija wannan wane irin saka abu araine kina bacci kina kuka bilkisu tafadi gami da girgizata firgigit ta farka gami da fadin innalillahi wa'inna ilaihi raji'un wai lafiya bilki ta kuma fade a kagare wallahi wani mafarki nai mara dadin ji to basai kin fada ba Allah ya maidashi alkairi ta amsa da amin ya kannaki ai yai sauki ta mike tana goge fuska bari naje na wanko fuskata ta fice daga ajin. Koda ta koma gida kasa bacci tai ba'abinda take tunani sai mafarkinta abincima dakyar taci fatanta kar Allah ya nuna mata irin wannan rana da nasir xai barta dan ita kanta batasan iyakar san da take masa ba. Yau kimanin sati guda ba nasir ba labarinsa duk ta tsargu tunaninta ya fara tafiya kanko munafukai sun kai masa labarine ta rasa waye wannan makiyin nata da yaganta da masoyi xaije sei yaga ya rabasu. Mai sunan manya wai tunanin mekike haka ne ta kakalo murmushi bakomai umma uhum maisunan manya kenan aiko bani na haifeki ba xangano kina cikin damuwa ballantana nasan duk wani taku naki kodai yaronnanne naga kwana biyu baya xuwa ko kinmai lefine dasauri ta dago kai a'a wallahi umma ba abinda nai masa baya dai garinne hakane to ki cire damuwa kinji nasan meke damunki anman Allah yana tare damu kinsan kowa datasa kaddarar tamuce ahaka tai murmushi nasani umma Allah baya dorama bawa abinda yafi karfinsa yawwa mai sunan manya. Umma wai yaushe Abbana xai dawo ne nimadai naga wannan karan ya dade mundaiyi waya yace asatinnan watakilma suxo da khairiyya da gwaggwo mansur yana makaranta gaban khadija ya fadi dan in akwai abinda bataso to shine xuwan gwaggwo kishiyar mamarta datake sakkoto da kanwarta wadda kokusa ko alama yarinyar bata bata girma ya kikai shuru uhum Allah ya kawosu lafiyq. Lah Abba yaushe kadawo ne kina makaranta kishiga gidan ina shigowa xakiga tsarabarki to abba yawwa xonan inkinshiga kome kairi xata miki ko halima kiyi hakuri kinji nasanki daman da hakuri sati xasuyi kawai to abba ta shiga gidan jiki asalibe. Assalamu alaikum tafadi da karfinta wanda koda na wajene xai jiyo ta shiga ke wannan wane irin iskanci ne ko ance miki nanma gidan karuwai ne daxaki shigi mana gida ba sallama umma nafayi sallama eyye to aiga makarya ciya ko wato nai miki karya kyaleta gwaggo kinsan kulama dan iska wani abune umma dake daki ta leko ke khairiyya ni nahaifeku na taba nuna banbanci kankune ta buntsuro baki ahankula tace wayasani ke nikike wa gunguni nifa umma nasani Allah kinfi san yaya dja eh nafi santa sekixo ki hanani santa karna karaji kinkiramin diya yar iska kinjini ko inba hakaba wallahi saina saba miki mara tunani kawai kinga saliha kinafa takurama yarinyarnan dan kawai kin haifeta. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Kiyi hakuri khadija ta dago ido dasauri dan mamaki bata tava jin ummanta ta kirata da khadija ba kaddarace baka wuce mata nasani umma kidaina damun kanki ni wallahi kullum inna tuna keda bava kuna tare dani inajin dadi dan nafi wasu basuma da iyaye yawwa kadijata. Wai khadija taxo jeka ce batanan kai jeka kace tana xuwa haba umma dan Allah kidaina sakawa ina fita wallahi hakan bakomai kejaminba se takaici sena saba da mutun sai ya gujeni nasani khadija kisa ranki cewar indai mijinki yaxo vaxai tafiba koda kuwa mexa ace masa kullum inai miki addu'a nasani addu'a bata faduwa kasa banxa balle ta uwa kan diyarta ta wanke hannunta datake wanke wanke ta sanya hijabinta ta fice Nasir ta hanga tsaye ya kurama kofar fitowa daga gidansu ido yako sakar mata murmushi tako hade rai alamar yai mata lefi sallamar ma aciki tayi barka da yanma tafadi shima dakyar ya amsa yana dariya lallai ashe mutuniyar ta iya fishi to ayimun afuwa nadauki lefina ya matsa inda suka saba xama tana kallonsa taki koda motsawa yafiskanci ta shaka da yawa ya ya taso haba tawan bama haka dake yakamata kixo kiji uxirina kafin kiyanken hukunci aikuwa innaji uxirin baida karfi hukuncina baida dadi yai dari hoo dija naji na yadda tabi bayansa. Nasani nai lefi dana ki xuwa aman balefina bane wallahi kinji na rantse banda lafiyane jinya nai banma xata xan tashi ba tadan kalleshi saima yanxu taga ya rame saitaji duk kunya ta rufeta da tun farko bata fiskanci ranar dayai ba aman kiyi hakuri kuma kema harda lefinku na baki waya kinki karva ta sauko daga kan tudun ta durkusa dan Allah kayi hakuri nice da lefi da nakasama uxuri yace haba dija meye haka dawo kiyi xamanki ai dabakiyi hakanba vaxan yarda kina sonaba ya jikin tafada jiki yai kyau ciwon kodata ne ya motsa ayya Allah yasawwake shiyasa na tawo miki da waya sauran kice baxaki amsava ko dan gaba madinga mgn dajin halin da juna ke ciki tai dariya nidai caxan karbaba xandai baka ta umma ya bata fuska kice kawai bakya sona ai ko wani yace maka bana sanka kace karyane aiko dai baxan kar yataba tunda gashi kinki karbar abuna ai daman se wanda ake so ake karbar abinsa irinsumu da ba'aso kuwa ya karyar dakai yadda yai yabata dariya au dariya ba kike bari na tafi ya mike kinga dare yayi bakajiba yadan juyo kabar ledarka kinsan Allah inbaxi daukaba vaxan daukaba saidai abarta anan ta mike ta dauka to nagode Allah yasaka da alkairi haba bakya bukatar godiynasu. Haka nake sani Na F.A.Ya'u Mai sunan manya wai waye yaxone nasir ne umna kinga harda hidima maxa mayar masa ta mike ta fita umma vaya nan to shikenan ajiye inyaxo ki fadamin. Khadija xoki fita inda sabo ta saba uncle mahfux kenan kotai magana ko bataiba sai ya koreta taxo giftawa stupid kai ada inya kirata stupid kuka take fiskanta datai hakan yaxame masa jiki yasanya ta dena damuwa danshi ko aiken mutun yai yadawo seyace stupid ta fiskanci inxai fada ba stupid ne yake xama xaginsa ba uncle sorry sorry pls may i enter sai ya kalleta ya harareta ya cigaba da aikinsa ita kuma taki daina bashi hakuri saida da yagama tsaf ya bada class work yaxauna ya hau mita wai ku ace duk yawanku mintina wajen goma kun kasa amsa tambaya biyu keni kin dameni shigi but karma kiyi aikinan dan baxan maka ba tashige batace komai ba xamanta vefi da mintina ba ta gama sanin halinsa yasa ta mikawa fatima ta vashi xatonsa na fatimane ya maka wow! I salute u gaskiya kinyi kokari banyi xaton akwai nai iya amsawaba uhum ashe kasan da wuya rukayya ta fada ta duba bayan littafin sekuma ya saki tsaki fatima come out kinajifa nace baxan maka ba ai bansan nata bane nadauka na bilkine uncle kenan uncle na dja yan baya suka fada who is that stupid ya fada gaba daya ajin aka saka dariya shima sai yasa fariya wallahi kun ranani ya dibi kayansa yavar ajin atika ta fito kunsanme class Allah guy dincan san khadija yake fadi ki kara fade suka saka shewa gani principal yasa sukai tsit. Allah in malan mahfux yace yanasanki kin more inji bilki hhh kinsan kuma koda wasa bantaba jin sansa ba kawaidai i respect him kyama fadi gaskiya inafa kallon kallon dakike mas Allah bilki baki da dama toni so ai nasiyar saidai so na abota ko na da da iyaye ohhhh nidai ince wannan wane mai sa'arne saranki a inuwa xaki ganshi kodai yan kishinne shiyasa ake boyeshi havadai banasan ai irinta Abdul ne se kowa yasanmu tare abu ya tarwatse gaka ne Allah ya tabbatar tace amin aminiyar tai lokonsu itama tai nasu. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Umma dan Allah ki bata bawai da wata manifaba na vata wayarnan ba nasani isa rike wayar ne batai ba dan Allah umma kiyi hakuri kabata shikenan naji bansan waya cikin dare kaji ko yawwa umma nagode xan kiyaye tana makaranta kasan sunfara lesson na waec to umma xan jirata baxaka gajiba a'a bakomi tace to aiko yaro yakarbar ma sallaya to umma ta shige ciki. Kasan tuwar tau baixo da motaba yasa bata gane yaxoba saida suka tsaya sukadanyi hira ita da umaima kafin tashiga gida umma na dawo yawwa yar albarka bakiga bago bane a'ina tahau duru duru a kofar gida auwwo ban kulaba ta ce bari na cire uniform din ta cire ta daura alwa ta leka suka gaisa xanyi sallah inba damuwa to ina jira tashiga ciki. Nabarka kai kadai ko ah vadamuwa taxauba kan tudun toya makarantar makaranta alhamdulillah kinsan me sai kafada daman naxone tunda watanni ya rage ki gama secondry inaso na aiko manya su shiga maganar taibshiru kafin tace amman fa inason cigaba da karatu da naso ko diploma ce in kammala ksfin aure yai dari karatun mace ba matsala ta bane sekiyi a gidana to anman yaushe muka hadu kinga dja kice kawai bakya sona bahaka bane badai naso mu rabune yai dariya kamar ya ka karan lokaci lokaci na nawa kuma. Yau nakesan bayya na maka abinda nake gudu yau xan bayyana maka sirrina tau xan bayyana maka asalina koni wace nasani ban kyauta ba tun asali yakamata na fada maka sanka ya hanani sabida tsoron fada maka xai xama ajalin tarayyarmu. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Hmmm khadija kenan kadijan nasir nasani khadija nasan mexaki fasan i know a lot about u u tunkafin na tunkareki nasan komai naki basai kin fadanba nayarda xan dauki ko wacce kadda da ta hauki nima nadauka ta xama tawa tadan kalleshi da gaske kasan me xan fada nasani khadija nasan ko badade xaki fadan shiyasa ban taba nuna miki nasani va tau da xance ya kama gashi na nuna to inkai ka amince iyayenka fa suma sun amince ba musu bayani sudin masu ganewa ne taji wani dadi ranta tabbas bata da kamar nasir a hankula ta fadi yana inasanska nima inasanki djana xanso ki ahaka yadda kike bantava taukan kaddarki matsalaba dan kema bake kika dorama kanki ba bani da kamarka bakuwa xan samuba yai dariya xaki samu fiye dani randa xaki ajemin yara rai dariya ai kaji davakai da van samesuba u will always be asaman kowa da nake ko natava ko xanso bayanka suke inkadauke Allah da manxo se ummana da abvana yai dariya djana takaina. Naji yanxu ina maganarmu ta tsaya kabari xan fadawa umma ta fadawa abvana komai yace xan fada maka to Allah tasa muji alkairi yau inada tiyqta da xanyi kimun addu'a Allah yasa ayi a sa'a amin bara natafi nasan ni suke jira sukai sallama ya tafi Koda ta koma gida ta fadama umma komai itana tai murna da abba yaxo take fada masa yace bakomai ya aiko. Magana tai karfi waec ake jira kawai su gama asaka rana. Ah lallai dole dja taki malaminmu tunda tasamu hadadden guy inji Aisha ke yanxu duk kwakwalwarki aure xakiyi Allah sarki xata tafi ABU mai labile mukuwa semunga mangwafa ahto kuma xama dictionary inji bikil shekara iyanxu munxama mama wayyo dija kin kwafsa to wai wayace muku baxan karatu bane oho tunda aka sanya ranarta tan group din nasu suka sanya ta agaba kowa da irin salon tata tsokanan. Koda waec ta fito tayi kyau kasantuwar vatai jamb va yasa nasir ya sayo mata form na nursing taje intro koda bata ciba tasamu experience kqfin next yasai mata jamb din. Biki dai ya kankama sauran sati biyu duka bangarorin shirye shirye ya kankama ankawo lefe anyi komai amarya tai kyau dan tasha gyara. Tunda satincan inta kira wayar nasir akashe duk hankalinta ta tashi yau dai tai sa'a amman mai makom taji muryarsa saitaji mace hello aunty khadija safiyya ce hankalinta yadan kwanta tunda tasan kanwarsa ce ina y nasir din ai vaida lafiya jibi ma xa'a kaishi india kodarsa ce ta tashi bata jira sauran amsarba ta fashe da kuka umna taxo da sauri lpy umma nasir me yasameshi beda lpy aikima xa'amai innalillahi kawai take fada umma inasan ganinsa jeki tawo da bilkisu ko Aisha su raka ki to umma ta mike ta fice. Kafin ta dawo umma tasauke kunin gyadar data dafa kawai ta juye mata a flask tana dawowa ta bata gashinan ki kai masa wannan ki hau mota wannan kusai lemo da ayava to umma suka fice kumai sannu. Hankalinta be kara tashiba sai yadda taga nasir din ya koma cikin yan kwanaki ganinta yasa yai karfin halin tashi umma tace yanxu saida da safiyya ta fada muku banasan hankalinki ya tashi nan suka gaisa tabar musu dakin aikuwa yasha kunun sosai kaxalika ayabar lemonnema yaki sha yakoji kwarin jikinsa. Sun dan taba hira wajen awarsu biyu suka mike bari muje yana Allah ya kara sauki ya yunkuro yanasan ya mike dan rakasu yaji gadon bayansa ya amsa cikinsa yai wata irin mirdawa vaisan sadda ya riko hannun dja va sannu kawai take iya furtawa idonta na xubda hawaye bayan yadan lafa masa yace khadija tace yana inaso ko bayan raina kimun alfarma kiyi karatu kixauna cikin farin ciki kinji ko kixama abar alfari ki nunawa duniya xamantowa irinki bashine karshen rayuwava yana kadeba fadin xaka mutu tare xamu rayu cikin farin ciki tare xamuyi gwagwarmayar karatuna xamu rayu rayuwa mai tsayi mai farin ciki kaji yana tadago baya ko motsi vata san sadda tau girgixashiba naji dija kidauki alkawari naji yana nadauka xan xamo mai cika maka burinka insha Allahu yawwa kadijata kisa aranki ni mai kaunarki ne inasanki khadija kuma xan cigaba da sanki har abada nasani yana nasa. Ahankula yake furta lailaha illallah can taji shuru safiya tayo kansa tana jijjigashi ya mutu tace kalmar data doki kunnen kadija kenan nan ta xube ko motsi batai safiyya tai waje aguje suka dawo da umma da y mansur hajiya ya mutu inda bilkisu ke fadin ta mutu wayyo Allah nai rashin Aminiya aminiya ta gari inda safiyya kefaman fadin wayyo yaya nasir kataimaka karka tafi hajiya kawai hawaye take tarasa abinyi nasir din ko khadija mai shirin xama sirikarta. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Nasir dana ne ga babban gida haifaffen garin kano unguwar galadanci shine na hudu kuma auta a gun iyayensa yayi primary da secondry dinsa a kano capital yayin da yai degree dinsa a BUK yayin da yaje Malaysia yai karatunsa kan kwarewa fannin fida wato dai shidin kwararren likita ne bayan ya dawone ummansu ta basho shawarar bude nasa asibitin da kudin gadonsa. Cikin sa'a kan kace mene wannan asibitin ya bunkasa tundawowarsa ummansa ke burin taga yai aure sai yace shi aure lokacine koda yaxo mata da bayanin khadija tai farin ciki sosai bata dauki komai game da bayanin da yai mata ba face tausaya ma kadijar. Dakanta taima kawunnansa bayani kasan tuwarsu masu illimi suma suka fuskanta fuskantar tasu yafi komai yima nasir dadi domin shi kansa yana mamakin yadda yake san khadijar yasani ta shiga ransa sosai. A wani hannun khadija... Haka Nake Sanki Na F.A.Ya'u. Saliha diya ce ga malan umar maxaunin unguwar yakasai yarinya ce data taso cikin nutsuwa ga farinjin jama'a tun tasowarta ta bude ido da san karatu kasan tuwar iyayenta ma masu san abinne suka bata goyon ba. Burin cigaba da karatu dake ranta yasanya taki baima kowanne saurayi dama domin bata san sansa yaxame mata cikas wajen karatunta duda kuwa burin kakanninta bai wuce a mata aureba. Yadda maharax ke mata yasanya batasan sadda ta fada kogin sansa ba mahrax irin yarannanne da iyayensu ke kawosu almajirta tun xuwansa yake gidansu saliha tun ba'a haifeta yayin data fara tasawane ya fiskanci lallai santa yake bai wata wata ba ya fara bayyana kansa bai wani sha wuyaba kamar sauran samarinta ta amince. Tun khadija tana ss1 wani mansur dan gidan wani attajiri ne yake masifar san saliha babu irin yadda baiba dan tasoshi aman baya gabanta. Wata ranar litinin ta dawo daga makaranta mayen nata yana cikin abokansa kamar ance ya kalli gefe ya hangota tana tawowa aikuwa ya mike yai inda take sinxo dabda inda abokansa suke taki kallonsa sai faman rokanta yake taja ta tsaya haba malan kai wane irin mutunne ance ba'ayi ance maka so dolene mutun sai kace maye haba khadija yaushe xance kidinga kirana inda abinda yafi mayene indai kan sanki ne kaga malan kaban hanya na wuce ganin baxai matsaba yasa ta juya dan bi ta daya lokon yai saurin riko hannunta aikuwa a xuciye ta jiyo ta kwada masa mari kaga malan inkanaji da rashin tarbiyarka da rashin mutuncinka karka kara gigin tabani kaji ko yayin da yadafe gurin hawaye na bin fuskarsa ta tankadashi gefe gami da kwace hannunta tai wucewarta ta barshi nan abokansa na mai dariya. Koda ya koma gida juyi kawai yake yakasa bacci daya rufe ido ita yake gani da lokacin data mareshi tunaninsa mai xai mata ya huce abinda tai masa yanasan yai mata abinda baxata tava mantawa dashi ba. Haba nawan yau naga baka fito bane yasa naxo inga ko lpy subhanallahi baka da lafiya kaidai bari Aboki damuwace nan ya fada masa abinda saliha tai masa ya fashe da dariya sabida wannan xaka damu kanka yakalleshi famida hade rai kaga malan inbaxaka tayani vakin cikiba to ka fice mun daga daki ko kagane yi hakuri maida wukar kafadan me akema mace mafi kaskanci wanda baxata taba mantawa dakaiba ka aureta ka daga nan ka gana mata axaba what baxan taba aurenta ba natsaneta wallahi tai min avinda ba wanda yataba yimun marina fa tai ta tofarmin da yau cikin jama'a haba khalifa wulakanci yakai ya fadi yana goge hawaye. Bada wuri take tafi makaranta ba eh maye hadin xuwanta sch da abinda tai mun ina bata yawo sai sch eh to inta fito xaka sa asatota indai kanaso karama abinda tama to ka kwace abinda tafiso me kenan ka mata fyade what zina fa kace eh fyade ne kolokuwar wulakanci da namiji xai ma mace yadanyi shiru anya xan iya haba sai kace bakaine mai dauko karuwaiba kasan wadannan sunyarda daukosu nai na biyasu hakkin wannanfa baya barin mutun seka xauna da bakin cikinta natabvatarma sanda kai mata hakan xaka huce. Shikenan na amince yanxu wane kake ganin xai dauko min ita Kabarmin komai a hannuna suka tafa shi yasa bake sanka wallahi. Yau talata da sassafe ta fito domin tanasan ta kammala duty dinta da wuri domin tashiga aji batasan take missing karatu unguwar tai shiru gabanta ke faduwa tunda ta fito daga gida. Dedai shekara Hamxa ya tareta kasantuwar tasanshi yasa tace haba hamxa maye haka tadan saki murmushin mugunta dallah ni malan ban hanya na fixe au nima rashin kunyar xaki mun kaga malam ni makaranta xani sannu dictionary ya dadi gami da danna mata tsimman da ke hannunsa aikuwa ta fada jikinsa yadauketa cak ya jefa bayan mota sai gidan da muktar yake tsula tsiyarsa dake xoo road. Gatanan sauran naka aikin yakalleta kwance kan kujerarsa ya rungumo hamxa kaga mamin komai wallahi bayan daukar fansa xan maida yawuna kasanme ba yanxu xan aikatata ba sai idonta biyu nafisan yakasance baxata manta daniba. Koda ta farka daga bacci taganta kwance kan luntsimemen gadon afirgice ta mike gami da yowa waje ta tsinci kanta awani tafkeken falo zaune yake idonsa arufe da alama tunani yake kamar a mafarki yaji tana cewa muktar daman kai kasa aka kawo ni nan yai dariya kina mamakine to meyasa ai basai kin tamvaya ba yanxu xan fada miki kinmun abunda ba'ataba mumba kema shiyasa nake san miki abinda ba'a taba miki ba kamarya xaki gane ne inaso kiban wannan abinda kikafi so ta fiskace shi dan haka ta durkushe tana rokonsa ya fashe da dariya ni lokacin da nake rokonki baki saurareniba nima banda kunne ya dauketa caraf sai uwar daki. Yaushe kake ganin xamu maida yarintar nan haba malan ai bayanxu ba wallahi saina moreta yai dariya kamar yaushe se randa ta isheni tukunna. Ga kayanan inxaki sauya kuma wallahi sauran kiki yin wanka naxo naji kina tsami ga maganinan kisha danki kara armashi haryaje bakin kofa tace muktar Allah ya isa abinda kamin yai dariya da be isava ya haliccemu. Gidansu saliha harsun fara cire rai yau kimanin wata biyar ba ita ba dalilinta yayinda naharax hankalinsa yafi nakowa tashi dan yanasanta sosai. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Kullum cikin addu'a yake da bin guraren yan sanda ko xa'a dace bayan mamarta gidan ba wanda ya damu da rashin dawowarta yanxu sunma koma sabgarsu har wani farin ciki suke kamar daman jira suke ta bace din. Bakasan wani abu ba hamxa sai ka fada yarinyar nanfa ciki gareta ya kake ganin xamuti da na yanke shawarar kira doctor Dernial yaxo ya zubda cikin inmaidata gida na wuce wallahi santa nake so nake ta yafe mun adaura mana aure What😳 yafada ya xaro ido kai wanne irin gaula ne ai in aka xubda cikin kamaidata gida baka ramaba bakuma xata taba aurenka va abu mafi sauki kamaida gida ta haife kaxo ka karbi abinda ta haifa ka kashe kaga kai mata tabo na har abada bamai auranta kaga nangaba ko ance ta mari wani xata tuna dakai kumafa hakane dan wallahi ko na aureta duk sanda na tuna ta mareni saona mata duka suka sanya dariya baki daya to yanxu yaushe kake ganin xamu maidata to dakaine kadaukota kabarmin komai. Daren talata wajen biyun dare suka shaga mata banju sai kofar gidansu anan suka yasar da'ita aikuwa da sassafe babanta yaxo fita unguwa yaganta ya sureta se gida yana kwalawa babarta kira Hadixa kina inane fito kiga ikon Allah tana barci taji kiran dasauri ta fito saliha ta gani kwance babu alamar rai ajikinta aiko ta fashe da kuka kukan ya taso da kishiyoyinta suka fito ana jajen ganinta. Kwananta hudu da dawowa har xuwa ganinta ake dakamakon cikin jikinta har ya fito har anfara yawo agari kan cewar aiba saceta akaiba guduwa tai gun saurayinta seda ya kunsa mata tsiya sukau dabarar dawowa da ita wanda kuma mabaruka kishiyar mamanta ita kebi gida gida tana fadin haka. Koda saliha tafadi cewar mubarak yasace akaje gun babansa saiyahau masifa kan dansa na garine baxai taba aikata irin wannan abuba daga karshema police ya dauko musu dakyar kanin mamanta yakarbosu. Haka nake sanki Na F.A.Ya' A gida data fito sai shewa da waka abin baga yaraba balle manya xaman tsakar gida ya gagareta kullum tana daki ummanta kawai ke tausaya mata sai mahraz dinta wanda burinsa kawai ta haihu adaura musu aure duda bai fadawa kowaba dan gudun yan sokiya. Duniya taima saliha xafi domin tundawowarta gidansu ya gagari babarta domin irin gorin da ake mata yarta taje karuwanci ta dawo da ciki kullum cikin bacin rai take intashigo daki saliha na kallonta inta xauna ba abindake inbanda sharar kwallah. Kwanci tashi ba wuya yau watan cikin saliha tara haihuwa ko yau ko gobe gori kam bakama hannun yaro har wank kida ake musu in ummanta tai magana ace bata isaba. Abinda akema ummanta yabi ya dameta umman nata duk ta rame tausayin ummanta datake ji baikai tausayin kantaba umman nata duk ta rame ta fuskanci bata jin dadi inta tambayeta sai tace bakomai. Saliha nasani anxalinceki anman inaso kimun alkawari ko bayan raina bazaki kashe abinda kika haifava inaso koma maine kibashi tar biyah kibashk illimi ta addini yadda xai xama abin alfari inasan ki nunawa duniya bawai yayan halak kawaine ne yaya na gariba to umma ai insha Allahu kema xaki gani lokacin kayya saliha nikadai nasan abinda nakeji araina xuciyata kamar zata fashe zaki samu sauki umma insha Allahu uhum saliha kenan. Umma kitashi kiyi sallah naga har gari yadan waye tafada tana shafa addu'arta shiru uhum umma kenan yau nauyin bacci kike ta mike dakyar tana ninke sallayarta kafin taje inda umman ke kwance ummah ummah take fade shiru ta jijjigata shiru sai hawaye umma dan Allah katki barni inkin barni yazanyi kamar antsikareta ta mike tai waje sai dakin mahraz dake bayan dayinsu kamar daga sama yaji bugum kofar adan tsorace ya fito ganinta yasa ya rikice saliha kafiya ummah na me yasameta ta mutu innalillahi wa inna ilaihi rajiun muje yace da ita mota yasamo dan suje asibiti. Kwanansu uku a asibi umma batasan inda kanta yake ba aranna hudunne tace ga garinku nan saliha tai kuka kamar ranta zai fita tasani Allah ne gadanta ummanta gatanta tarasa mai santa. Bakwai ga mutuwar mamarta tafara tabbatarwa tai rashin mai santa domin bawanda yake kula da cikin dake jikinta balle duk aikjn wuya ita keyi ta xama kamar baiwa agidan. Satin ummanta uku da rasuwa cikin dare ta haife diyarta mace taci wuya haka ta daure ita taima kanta komi ta gyara yarinyarta cikin daren ta tafasa ruwa da take akwai wuta tai wanka taima diyarta kasantuwar babu abinda ummanta ta rageta dashi na aikin gida duk ta iya komai akwai adadin danma bayan mutuwar unmanta kishiyoyinta sun dauke wasu abubuwan dan haka ta hada shayinta mai kauri tasha taxauna kawai tana bin diyarta da kallo duda bata hanyar halak aka haifetaba wani irin santa taji yana shigarta babu ta yadda xa'ai ta amince akashe mata ya koda kuwa ummanta batai mata wasiyya da hakan ba. Washe gari da safe ba irin abinda bata shaba har xuwa ganin shegiyar yarta ake sunan da yan unguwarsu ke fada ma diyar matsalal. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Kwananta biyu da haihuwa aka xugo mahaifinta yaxo tana murna dan rabonda ta ganshi kotaga yashigo dakinsu tun dawowarta da akace ciki gareta ya tsangwamesu yakarbi yar yagani jim kadan taga ya mike da ita xai fita baba ina xaka da ita yaja ya tsaya au da kina nufin xaki xauna ki raini ciki gidana ki raini ya gidana wallahi baxai yuwuba kasheta xanyi me wallahi inasan yata to baki isaba mara mutunci ta fashe da kuka yai waje abinsa aikuwa tabishi tana kuka tana rokonsa kasantuwar darene gari yai tsit yasa sauran jama'a suka jiyo kukanta dayake dakarfi take kuka tana fadin dan Allah abba kabarmin diyata Allah inasanta bata da lefi yana tafe tana binsa beko jiyoba kukan yai yawa yasa aka firfito aikuwa dattijai sukai masa ca aka malan tukurne ya karbe yar ya bata shi kuma suka hau masa nasiha yace indai har baxan kashe yarnanba to wallahi baxaunan gidaba malan tukur ya ce ta debo kayanta ta dawo gidansa shikuwa sukai tai masa nasiha yaki yace yafa rantse kuma ko bayauba sai ya kashe yarnan cikin makotan wani yakaima yansanda washe gari sukaxo suka tafi dashi aikuwa unguwa ta dauka saliha takai karar babanta kan shegiyar yarta alhalin bama tasan anyiba a police station akai masa katanga da yar ksn komai yasameta shine . Dakanta ta radana diyarta suna sunan ummanta tasa mata wato khadija take kiranta da mai sunan manya satunta biyu da haihuwa mahrax ya bujuro da maganar aure taki amincewa sakyar yasamu da taimakon Allah dana matar malan tukur ta yadda ananma mahaifinta cewa yai shi aiya sallamata yabarma malan tukurdin dakansa ma yaje yasamu iyayen mahraz dake kauye ya fada musu komai dansu hana dansu auranta aikuwa ba shiri suka tawo birni. Duk yadda sukaso hanashi auranta yaki sunja yaja daga karshe suka sakar masa dole sunaji suna gani aka daura auren saliha da mahrax auren sa kadauke ango da amarya ba wanda yai farinciki cikin sauran danginsu. Kwananta aittin da biyu da haihuwa ta tare a gidan mahrax tare da diyarta wadda tai dan wayo duk wanda yasanta yasan muktar to sai ya yadda sunada alaka dan duda kasantuwarta jaririya aman kamar ta baci. Kadija nada shekar biyar ta haifi diyarta muklisa dan da harsun fara fidda rai lokacin da muklisa ta isa yaye dangin babanta suka dauketa wai baxasu bar jininsu hannu mara tarbiyaba. Lokacin da khadija ta isa shekara bakwai xata shiga primary mahraz takaita makaranta shi yai mata komai basusan wanda yaje yasanar da iyayensaba sai gasu bala'i kala kala daga karshema takaiga babansa yace indai har bai cire sunansa jikin sunan khadiba Allah ya isa bai yafe masa ba kasantuwar mamarsa ta rasu tun yn yaro saliha dakanta tarokeshi ya hakura acure mahrax daga sunan khadijar to kisa mata sunan babanta tai murmushi abinda baxai taba yuwuwaba vaxan taba danganta tadashi ba kokasan nasan hardashi amasu san avvana ya kasheta nasan mexanyi dakanta taje makarantar duk wani takaddu nata ta maidashi Khadijah Saliha Yakasai ko sunan babanta bata saba dan tana gudun wata matsalal. Haka Nake sanki Na F.A.Ya'u Khadija na aji biyu a primary ummanta ta sake haihuwa ta haifi danta namiji murna gun kadija ba kama hannun yaro tayi kani tunda akai haihuwar burinta ranar suna taxo tai fati abbanta da kansa ya sayo mata abinda xata raba Ranar suna yaro yaci sunansa yasir sedai abin haushi duk dangin abbanta da sukaxo suna hantararta sukai tayi fatin ma datai ta doki karshe bataiba domin aranarma xaman gidan gagararta yai dan duk wanda suka hada hanya daga mai xaginta sai harara sai duka ummanta dakanta tace ta tafi gidansu Aisha ta xauna duda itamadin adarare take domin irin habaicib datake kwasa. Haka tanaji tana kallo suka soye naman suka kwashe suka kara gaba dashi domin dangintama ba'a maganarsu bawanda xatwce cikinsu yataba takowa xuwa gidanta yan uwan ummannata ma sun gujeta. Ummana na'am yatagari wai meyasa yan uwanmu basa sona kece baki musu abinda suke so Allah umma inai musu kawai basa sona ne sunasanki mana to umma meyasa suke dukana se sudinga cemun mayya shegiya mara uba bacin ga abbana nan batambayeshi yace shine abvana hakane umma to xai miki karyane a'a anman amma me kinfa fara isata da soki burutsinki. Haka Nake Sanki Na F.A.Ya'u Khadi na primary 4 yasir yayi wayo sun shaku sosai tana san yaron komai tasamu yasir dinta tana dawowa daga makaranta ina yasir dinta seta ganshi xata ci abinci. Ranar alhamis kanwar mahrax taxo dashirin tafiya da nasir shima baxasu barshi gurin saliha va aikuwa tace batasan xance ba karshe mahaiyin mahrax dakansa yaxo ya dauke yaron yana kuka khadija na kuka saliha na kuka. Zamtowar saliha mai kwakwalwa yasanya aka xabeta cikin masu xana jarrabawar tafiya secondry wannan shekarar murna gurinta kamar mai taxo tasamu ummanta ummana dan Allah so nake kiyarje mun kadija saliha da'ake cemun ya koma kadija S yakasai sabida me bakomai umma kawai nagaji da gorin da'akemunne ko kuma kina kunyar hada sunanki da sunana ba Allah umma ba haka bane to indai ba haka bane yadda banji kunyar hada sunanki da sunanaba kidaure kixauna yadda nasanya miki to umma. Umma na'am xaki fara tambayarne ko umma dan Allah ki fuskanceni ki daure kibayyana min ni wace koda naji sauki araina na wasu abubuwan da akemin nafara dena yarda da anakirana da sunan mamata ne dan wai kun rabane ke kindaukeni abba ya dauki mubarara ne ke khadija ni kike fadawa haka kina nufin mudin makarya tane xamu maki karya ko haba umma bankaiba bakuma xan taba kaiwaba daxan kiraku da makaryata wannan shine kuskure mafi girma daxanyi ki yafe min ta fada tana kuka tausayin diyar tata ya cika ta shikenan khadija na yafe kamarta Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Wata sabuwa yan matar baban mahrax ce tace babsnsa ya kamata sumai aure dan xewarta saliha ta mallakeshi dakanta ta fiddo da matar wata yar yarta ce sekawai kiransa akai wai anmai aure kuma so suke yaxauna da ita a garinsu wato sakkoto. Auren yana shekara guda aka bata yar da saliha ta kuma haifa akai sa'a kuma ita bata haihuwa aikuwa tadau san duniya ta dorama muklisa dan haka yarinyar ta taso asangarce kiyayyar duniya sun sakamata ta khadija dan haka tabi ta rainata. Wani irin xaxxabi saliha take hartake xaton baxata tashiba hakan yasanya yau tasa khadija gaba tabata labarin samuwar tare da rokarta ko bayan ranta baxata shiga ko tai abin lalaci dan xamtowa ansameta bata halak ba kadija tai kuka ta godema Allah domin ita tanama da uwa tasan danginta koda basa santa ga abbanta da yaxame mata garkuwa wani yananan burinsa ace yanada uwar yasanta koda ita tafi kowa duniyar lalaci anman baisantaba data haifeshi jefarshi tai bai san kowa nasava ita kuwa fa tasan kannenta ta rayu gaban ummanta tai mata tarbiyya ta sata makaranta tana santa tayi duk yadda xatai dan ganin tarayu itako mai xatace ma ummanta banda godiya banda tai mata addu'ar aljanna....tasani duniya bata da kamarta. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Kadija na SS1 ta hadu da wani saurayi inda suka kullah soyayayya khadija nasan Abdallah sosai sun shakuwa mai yawa har sunajin rabuwa da juna bamai yiwuwa bace tana ss2 Abdallah ta turo da iyayensa kan tanayin candy xasuyi aure duk wanda yasan khadija yasan abdallah dan makarantarsuma wataran tare suke xuwa ko ina take yana nan. Ranar asabar ranar dabaxata taba mantawa da itaba ta dawo daga islamiyya ta tun daga farkon lokon ta gango kofar gidansu cike da jama'a da sauri ta karaso abinda idonta da kunnenta suka gani yasata fashewa da kuka yan uwan abdallah ke sirfama ummanta xagi ta uwa ta uba ita kuma tana basu hakuri wai anaso danfari dan uwansu ahadashi da mara asali a hankula ta karasa ta ja hsnnun ummanta umma ki daina basu hakuri daman Allah yai Abdallah ba mijina bane da mijinane ko mai xasuyi sai na aureshi ki kyalesu Allah yana tare damu nasani addu'ar uwa bata faduwa kasa banxa kicigaba damun addu'a takalli daya daga xukinsu kusa aranku ko gawata baxata auri abdallah ba yadda in aka mutu ba'a dawowa haka nabarshi taja ummanta suka shige sukuma suka cigaba da xage xagensu. Tun daga sannan duk wanda yaxo bama tavashi fuska tasa ma ranta karatu xatai sai Muhammad wanda nacinsa yafi karfin tunanin mai tunani dakyar ta amince suka kulla sosayya aikuwa dai shima rabuwar tsiya akai duda abinda iyayensa sukai baisa yabarta ba dan shi yace ko su yarda ko kar su yarda sai ya aureta ummanta ganin halin data ke ciki cikin dangin mahrax bataso yarta ta zama cikin irin wannan halin yasanya ta kira muhd da kanta tai masa nasiyya dakyar ya hakura karshema sai barin kasar yai. Duda yadda khadija taci burin dena soyayya segata dumu dumu cikin kogin san nasir wanda takejin invashi baxa iya rayuwaba tanasansa fiye da kowanne saurayi datai yasota lokacin da kowa yakita danginsa sun nuna mata kauna basu taba nuna cewar dan taxama Shegiya mara uba itadin abar kyama bace face maraba da akullum suke da shigowarta family dirakota. Haka Nake Sanki Na F.A.Ya'u Cigaban labarin A hankula khadija ta bude idonta yayin da ta dorasu kan bilkisu sai ummanta da ke gefe cikin yan dakiku ta tuno da abinda ya faru xumbur ta mike daga kwance yayinda ummanta da bilki sukai kanta umma Nasir tana ina karku fadamin ba mafarki nake ba yi hakuri kixauna umma dan Allah karki fadan dagaske nasir ya mutu be mutuba khadija yana nan da ransa yana samun sauki wata ajiyar xuciya ta saki ta koma ta xauna. Safiyya ce tashigo suka gaisa da umma ya mai jikin jiki dasauki daxuma ta farka to Allah ya kara sauki daman aunty Aisha ce tace na rakotai mata gaisuwa tamata yajiki uhum har yanxu batasan da rasuwar ba jira nake takuma farkawa sai mu fada mata to gashi sauri take kar aita xuwa mata gai suwa bata nan to shikenan suka koma. Yau kwanan khadija uku a asibiti tawarware bata da magana sai abarta tage ta dubo nasir umman nasir din tace kar afada mata batun rasuwar sai ta war ware. Khadija na'am umma ta dago ta kalleta jiyo sosai mgn nakesan muyi ta hankali kinji ko to umma kinyarda da mutuwa ko eh umma inaso kiyadda da kowacce irin kaddara daxata sameki mai kyau ko maras kyau nantai tamata nasiha kafin ta fada mata rasuwar nasir khadija tai kuka bakadanba harta godema Allah. Washegari da kanta tashirya umma xanje inma maman nasir gaisuwa to maisunan manya saikin dawo tafita tunda fargiyar gidan data hadu da jafar yayan nasir suka gaisa tai masa gaisuwa ya nunata ga sauran dangi maxa mai makon taxama ita take musu gaisuwa sunema suketa mata gaisuwa ba'abinda take sai share hawaye dan ko anan tasam tai rashin dangin miji masu santa kaxalika cikin gida daga masu ya jiki sai masu ya hakuri. Sati ukunnan da rasuwar nasir inkaga khadija sai ka rantse tayi jinyane nashekaru yadda ta rame ta jeme kullum taxauna bata da tunani sai tunanin nasir dinta. Tayadda mutuwa gaskiyace in an mutu ba'a dawowa saidai ta kasa yadda nasir dinta baxai dawoba. Kinsan Allah bilki banasan xuwa islamiyar nan wallahi sabida me kawai na hakura da ita ne itace sanadiyar haduwata da nasir ko uniform din nagani wallahi tunawa nake dashi haba kadija ki yadda da kadda ra kece fa mai fadama mana ur present situation is not ur final destination dan Allah kitaso mutafi ko shi nasir din natabbatar miki wallahi baxaiji da ace sanadiyarsa kinbar neman illiminkiba shikansa xai xamto mai alfahari dake ta dauko mata hijabin dan Allah saka mutafi kin riga kin cuceni kince Allah muje umma mun tafi to Allah ya bada sa'a harga ranta taji dadin yadda tashirya xuwa islamiyya. Tun daga nesa tahango wata dalleliyar mota a kofar gidansu towa baki mukai ta fada aranta lah yah jafar kune eh nida mamane tana ciki daman gobe xan koma shine nace bara naxo muyi sallama naji mama xataxo nan to aiko ka kyauta nagode suka dan taba fira ta shiga gida mama ta karbeta da farin ciki suka gaisa ta tashi tashiga tabarta ita da umma kafin taji umman ta kwala mata kira taxo taxauna kusa da ita daman gurinki naxo batun admission dinki ya fito shine naxo karbar photo dinki se hawaye haba khadija kixama mai dauriya mana nasani anmiki mutuwa anman karki mantafa nima nasir danane kidaure mu hada kai mu cika masa burinsa yanaso kiyi karatu tun yana da rai yai konai kan makarantar nan taki abinda xakiyi ki anganar dashi shine kimai addu'a kiyi karatunki yadda xaki samu damar anfanar da duniya xai xamo mai alfari gareki to umma bari na dauko hoton. Yanxu kinga xaki fara xuwa sch of nursing din kafin lokacin jamb kiyi komai xai tafine yadda ya tsara naji safiyya nacewa yanasone kixama pharmacist ko tai shuru insha Allahu xaki xama kinji ko khadija inasan kimin alfarma ki cire damuwa aranki ki daure kiyi karatu ki cire soyayya kinji ko khadija to mama yawwa yarinyata ta mike ni bara na wuce umma dai bata da aiki sai xuba godiya har jikin mota khadija ta rakota. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Khadija ta warware tana sabgoginta sai dai wani abu dake damun ummanta shine yadda tafito da wata sabuwar halayya inta dawo daga makaranta sedai ta fita ta shigo da ita dan kuwa xamanta take kan tudun da suka saba xama in nasir yaxo gunta haka kawai ma saita faki idon umma tai waje ada ta xata gidan su Aisha take xuwa daga bisani ra fiskanci xama kawai take tai ta tunani dan wani xubin taddata take tana hawaye wani xubin tana murmushi abin duk yabi ya damu umma tsoronta kar abin yataba kwakwalwae diyar tata. Khadija anfara makaranta hakan takara dauke mata kewar nasir ta dage sosai tana karatunta intai kamar baxatai ba sai ta tuna da alkawarinta da nasir ta tuna karamcin family dinsu tai karatunta. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Kharatu kam yai nisa sati daya ya rage khadija su fara introductory examination karatu take ba da wasa va dan yadda taga kowa ya dage burin kowa yaci hakan yasa itama din tadage ba wasa baccima yaxama ragagge gareta. Kwanci tashi yauce ranar daxasu fara exam hankalunsu duk atashe yake yadda ake tsoratasu game da exam din ga wani irin sanyi da'ake xubawa kowa kagani da'irin addu'ar da yake furtawa bakinsa. Khadija nadaya daga cikin wanda suka riga kowa gamawa da alama paper din tai mata dadi yadda take ta sakin annuri afuskarta kai tsaye tuka tuka ta wuce tai alwala sannan tai masallaci aiko kafin ta fito har yacika da dalibai wanda suka gama sai faman tsinema malan suke itadai takallesu tai dariya.ta mike Rahma xo mu wuce ko sai kin huta ke ina wani hutu paper din gobema yar kantace hakane fa gara muje itama dai Allah yasa tafi wannan amin khadija yawwa tun dazu nakesan nace miki mubi ta Aminu kano xansayi sako kai rahma wallahi kinfiya san yawo da wahalar da mutun ina daxune kukaje Aminu kano din keda su asiya dabasai kisayoba ke matsalata dake bakya ganewa wadannan kwadayayyun inna sayo aicinyewa xasuyi subarni da wallahi tallahi to shikenan daga nan nasai rake. Aisaiki shiga ki sayo au baxaki shigaba wallahi baxan shigaba kafin ki fito ai na rage wani abu uhum uwar wayo sauran kuma ki tsaya surutunnaki da wannan dan rainin hankalin owwo nagano ki bukuli kike min dan kar aban kyautako shiyasa baxaki shiga ba ko eh naji komai xaki ce sedai kice baxan shigaba aiko sai nafada masa Allah xakisa nai tafiyata yi hakuri naga alama xancen kike so nabaki minti biyar inbakixoba kyatafi ke kadai tai dariya ta shige. Kinsan ya mukai da mutumin mtss wallahi Rahma ke matsalace halinku daya da bilkisu kullum haka kike cewa xanso naga bilkinnan taki saka ranki a inuwa xaki ganta af kinga nasha'afa har kwatancen gidanku naimasafa kutt....mai kikace ainasan kinji haba rahma bansan iskanci danme xakimin haka ta bushe da dariya ashe kin iya xagi tai tsaki kinga inaganin mutuncinki meyasa xakimun haka ohooo na fiskanci bakida tausayine shiyasa haka kikace ko fuuuu tai gaba Rahma na binta tana kwala mata kira bata ko jiyo ba dadan karfi tafada dan Allah khadija kitsaya kiji taja tatsaya aibansan gaka kike da xuciyaba wallahi da wasa nake banma ganshiba sai alokacin ta saki murmushi haba harnaji dadi itama tai dariya ayimun hakuri da vata miki rai danai naji na hakura but kussure mafi girma daxakiyi shine ki yi abinda kikace yau kinyi Allah nadena kulaki tai dariya ai vama xanyi ba wai daman hqka kike da fada tai dariya kama take kinsan kowa ya iya iskanci tsoron Allah yake sawa kar ayi Allah ko eh mana dabadan hakaba wani ustax din inyace xai bude babin nasa rashin mutuncin ai sai dan iska ya rike baki dan mamaki. Komai yai farko xai karshe domin yaushe ranar karshe yauce zasuyi instrumentation paper din karshi jikinsu dik amace yake yan hostal sai hada kaya suke wanda xa'axo dauka anata xuwa diban kaya. Kai gaskiya yaune mukai intro wannan paper din da wuya take kedai bari rahma ni bama wuyarba karar da ake daka mana tafi komai raxanani uhum ai basa kyautawa aikodai anmanfa muma munada lefi in ance move sau daya bama matsawa ai daman ke haka kike bakya yarda da lefin malaminki anman ko kiyarda ko karki yarda wallahi basu da mutunci malaman sch dinnan nidan Allah bar xancennan muje muyi sallah sukai alwala sai masallace. Masallacin cike tayake da dalibai masu kwalliya nayi masu hotuna nayi rahma taso mutafi haba khadija kibari muyi sallama da mutane mana bakya ganin daga yau shikenan hakane wani se alahira xamu sake haduwa yawwa ko kefa kinga bari naje muyi sallama da Abba nasan balallai mu kara haduwaba ta fice tabar rahma suna hotuna. Dan Allah kixo muyi pic ko dayane Allah baxanba toshikenan yanxu sai yaushe sai sanda Allah yaso to shikenan Allah yasadamu da alkairi ya shiga motar da suka lodama kaya yana dago mata hannu Abba kenan xanyi kewarku ta fada ahankula. Gindin bishiyae mai rake taja taxauna dan yau yatashi tana bin sauran dalibai daketa warkajaminsu da murnar kammala intro da ido batasan sanda hawaye yafara biyo idontaba dan tunawa da nasir dinta yaugashi kamar bai rayu cikin rayuwarta ba gakuma yan ajinsu sunyi xaman mutunci sun rabu suma wadannan din gashi sun rabu ba lallai su kara haduwaba jiyai andafata dasauri ta goge hawayenta haba kadija dan Allah kixo ko hoto dayane ai dake dasu maman baby muje tace dan batasan doguwar magana dan Allah rahma mu tafi magariba ta kawo kai sukai sallama da sauran sukai hanyar fita dan Allah tayani na tsinki magaryar nan Allah baxan tsayaba kinsan xaki tsinka kika tsaya hotuna tai dariya dama wasa nake kimayi da gastasaba Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Yawwa khadija jiya kina islamiyya mama taxo tace yau kije tanasan xakuje kuyi register din jamb to umma bara nagama wanke wanken kuma karki dade kinsan gobe xamu tafi khatsina ko khatsina umma eh ko harkin manta eh umma kiyi sauri karmuyi dare toh umma tafada badan ranta yasoba dan batasan xuwa dangin abbanta. Yanxu nake cewa safiyya taxo taje ta tawo dake ko umman ta mance bata mantaba aikine yamun yawa toshikenan bari safiyyar tashigo sai kuje nannan ne ba nisa to mama yakuwa batun intron taku bata fitoba har yanxu to Allah yasa muji alkairi amin mama anmanfa duda haka kidage kici jamb dinnan degree yafi diploma kinji ko insha Allahu to wanne course kikeso eh to dadai nafisan pharmacy anman ance va'ayi a kano nasan kuma umma baxata yadda da xuwa xaria ba tokiyi murna anfara ai bara suka fara kinga saikisaka shi inkin samu sai kibar nursing din ko dai kinfi san nursing din a'a wallahi to shikenan Allah ya taimaka tace amin.sai mundawo to sai kun dawo yawwa mama ni xan wuce daga can umma najirana xamuje khatsina a'a kibiyo tanan xan baki gudunmawa kikaima amarya danma danma dai akurarren lokaci nasani aida muje tare tai dariya hakanma mun aiyayi Allah yasaka da alkairi amin kije karsu rufe sutafi sallah. Tunda suka isa garin gabanta ke baduwa dan tasan xuwa garinnan baya tava xame mata alkairi indai sukaje da bakin ciki take dawowa aikuwa kamar tasani yawdinma da abinda aka fara tararta kenan gaisuwa take anman in dutse ya amsa gwaggwo ta amsa. Yawwa gashi inji mamar safiyya tace abaima amarya gwaggwo takarva tana yatsina fuska amvulance wanda yan dubu dubu sabbi na dubu hamsinne eyye wace mamar safiyyar umma tai saurin cewa itace wadda da xata auri danta ohoo to angode khadija dake gebe arakube gwaggo wai ina amarenne ta kalleta a kaikaice bansaniba karma kiyi xaton kudinnan xaisanya nafasa halina kimaji da wai yadda basan ganinki nakeba bakuma san xuwanki nakeba karki sake kishiga cikinsu kije kishafa musu tsiya haba gwaggo kanwarta fa akema biki ace baxata shiga sha'anin bikinba eh aishiyasa nace kartaje gunsu balle ta kashe mata aure yaran yanxu da xalinci tunda ita bata samuba haba gwaggo taya xa'ai tai haka kinga saliha inkinga bakyasan abinda ake mata ki maidata gida kema din dabadan karaba kasantuwarki uwar amarya walkahi dabasai kinxoba ah nima abune mai sauki sai intafi ai to kitafi sai mai. Lah yaya yaushe kukaxo tundaxu inata xuba ido inganka muma jiya mukaxo kinga amaryae kuwa a'a aiko tunjiya take mita bakixoba tai dariya gashi ainaxo kixo na rakaki inda ake mata kitson kema se'a miki a'a ni bakowa kekaman kaiba todai kixo muje kugaisa kaga yanxu mukaxo nagani sosai kavari intaxo ma gaisa.To ai shikenan xokaban labarin makarantarku yai dariya bana xamu shiga ss1 ta budo ido kai dan Allah wallahi gaskiya na tayaka murna jai muhd maye haka sukajiyo muryar muklisa menai banace maka ko khadija taxo karka kulataba ankukata din ba yayarmu bace haka kace eh haka nace to wallahi saina fadama gwaggwo kifadadin kaida mabruka bakuda aiki se wani fadin yaya kadija bacin ance ba yar mu vace kyaji dashi banxa marar hankali ni kake xagi ko anxaga ta biyoshi ya mike aguje yanadari wallahi bakida hankali kina mace kina gudu xan kamakane ta juyo ta gallama khadija harara tai dariya inda sabo tasaba. Haka Nake Sanki Na F.A.Ya'u Lah yaya yaushe kukazo tun dazu aimun dan jima shine bakixo gunaba yi hakuri kanwata gajiye mukaxo to shikenan yanxu taso muje amaki fulawar biki dan baxai yuwu bikina guda ace babbar yaya babu fulawa a bikin kanwarta ba hooo mabaruka ni na isa wahalar da amarya kije ki huta yasir ya rakani haba yaya dan Allah kitaso muje naji xanje kije kici abinci kafin sannan na huta to to shikenan. Yawwa gwaggo ga yaya mabarukar nan yawwa mara mutunci daman ke nake jira naji ance xaki dau waccan mara mutuncin kikai gun mai fuwala to ahir dinki ta turo baki wallahi sai nakaita ai yayatace yayarki fa kikace a gidan ubanwa taxama yarki kufa kukace ummanmu ta haifeta aiko ba ita ta haifetaba tunda tanasanra tana kuma xaune agunta mutunci yasa ta xama yayata ai gwara da kikace mutunci ita wannan yarinyar daga ita har uwar tata ina sukaga mutunci haba gwaggo bafa nasan abinda kikemana wallahi uwa fa uwace danme xaki dinga cin mutuncin ummanmu gabanmu eyyye ah lallai kin rika todama banda abinki gwaggo yaushe barewa xatai gudu danta yaki aitasha a nono ahto nidai nafada muku yaya khadija yayata ce umma kuma ummata ce inaso kusani ban hanaku abinda kukeba but duk wanda yai agabana yadda baiji kunyata ba baxanji tasa ba fuuu ta fice itadai gwaggo ta rike baki ah lallai kin isa. Yau ake yini kowa kagani sha'aninsa yake amarya tayi kyau har ba'a fade koya ta juya bataga khadijava nan xatafara nemanta dan batasan abinda xai bata mata rai. Waya cemiki nan gurin karuwai ne daxaki kwaso tsummokaran kafafunki kixo inna ta fadi dallah matsani kiban guri se anai maki fada kidinga wani sin sin dakai kamar wata tagari da'ace uwarki nada xuciya da tuni ta daina kawo mana ke danginmu yi hakuri kawai tace eh aisai ancuceka ace xa'abaka ni wallahi fatana ma kar itama ta lashema wani cikin yayanmuvkurwa kamar yadda uwarta taima mahrax ya aureta ina aibaxai yuwuba in ita ta auru shegiyar yarta kam kwalelenta da danginmu. Yawwa yanxu kawar amarya xataxo ta bamu takaitaccen tarihin amarya sukajiyo ta lasifika gaba daya suka bada hankalinsu komawar zainab kawar mubaraka ummi kanwar baban amarya ta amsa nan tafara xubo nata habaicin da duk wanda tasan umman khadija yasan da ita take hakadai sukaita cin mutuncinsu bakin cikine ya ishi kadija da kuka tabar gun bikin gurin. Yaya yanaga kin fito ba'a tashiba wallahi gajiyanai khanina kinga kuwa nima na gaji inkina da kudin mota xo kawai mutafi tai dariya to shikenan anman jekakafadoma amaryar mun tafi dannasan xata nememu in antashi to angama babbar yaya ya shige gurin tace to su fito ita da yasir suna tafe suna hira abib sha'awa tanasan kannenta duda kadda tasanya basu zauna tare ba dan Allah babbar yaya ki taimaka karmu koma gida muje kidan saimun kayan nakulashe tai dari kai yasir kana namiji kana kwadayi yaya kenan baxaki ganeba aishi dadi kowa yanasansa uhum lallai naka wasane ince dai kana dagewa wajen karatu ta sosa keya sosai aiba dakiki irin yaya muklisa tasanya muginta cikin ranta shiyasa wallahi nai murna lokacin daxan shiga jss da'aka kani Borden na huta da duka ita kuma ta huta da rashin jinkafa Allah baki gane bane ba'abinda nake mata yo yanxu bagashi ta wuce ba hakane kuma sedai ta daki yayanta yasir kenan sarkin shirme hava yaya kinafa maidani baya ss student ne fa af yi hakuti na manta da dan jami'a nake mgn suka saka dariya baki daybanu Haka Nake Sanki Na F.A.Ya'u Yau khadija jinta take cikin annashuwa domin sun kai amarya yau xasu dawo duk ta hada musu komai da nasu umma take jira kawai taxo su tafi duk ta kosa danma batasan tace ta tawone dan tasan yanxu xa'ayo kanta. Wayyo dadi anya kuwa kece Rahma ashe rai kanga rai yar rainin sense aikya fadi haka ke ko awaya va'ajinki uhum nidai bar wannan batun shigo shigo wayyo nai missing dinki da yawa tai dariya bari na fara gaida umma danni dan ita naxo badan keba dan datakene kisha xamanki to invanda abinki dan wa kikasan umman suka gaisa da umma dayake tasanta asuna bayani kawai tai mata ta ganeta Allah kinmin baxata bantaba xatonki ba kedai bari gajiya nan da xaman gida nace bari na gwada xuwa koxan gane kwatancennaki aikodai kin kyauta sosai wallahi naji dadi suka sha firarsu irin ta jawaye.. Umma xan rakata anman xan biya da ita ta gidansu bilkisu xasu gaisa ta sai kindawo rahma agaida umma ta ta hado kayan da ta hata mata gashi kibata to umma angode suka fice. Yau gani ga rahma inji biki ai inashan lavarin rahma ta fada tamace halinmu dayane tai dariya nina haka tacemun duda banyarda ba suka saka dariya baki daya. Ke ban fada mikiba Rahma ta fada har sun tsaida mata da adai daita sahu tace yi hakuri malan ba hawa xamuyiba to aku sarkin magana wacce gulmar kuma aka samo mutuminki ma kadija ta gintse fuska zaki dara ko kinga rahma bani nasha inji bilki ke ai kamu tai gayen ya hadu kullum damuna sch se yaxo guntata taki bada fuska shine naje asibiti amakare naje anman yana ganina ban wani sha wuyaba nida nake dorin dosano bilki tace batta saitaje tana kallon ruwa kwado yai mata kafa kinga insansa kuke seku fadan inmuku hanya suka saka dariya inxaki iya ba kinga rahma kin gama dani wallahi tunda kika fadama wannan sarkin damun ai na banu Haka Nake Sanki Na F.A.Ya'u Cikin ikon Allah exam dinsu khadija tafito inda tai sa'a tana daya daga cikin wanda suka ci farin xiki gunta ba'a kama hannun yaro duda tawani fannin bataji dadi ba kasantuwar vabu rahnanta cikin wadanda suka samu nasara har kwalla tai yadda rahma taci burin xama nurse. Karatu ya kankama yau satinsu biyu dan har sunfara shirye shiryen tafiya asibiti kadija duk ta damu domin tana kewar rahma sosai kasantuwar duk wadanda suka ci basu wani saba ba wasuma batasan dasuba. Tunda suka dawo take ganinsa kusan kullum saita ganshi ya shigo cikin makaranta bata taba barin sun haduba dan batasan takura. Satinsu daya da dawo dawowa daga asibiti aka kafe yan replacement mutum biyar ciki harda Rahma aiko murna gurin khadija ba'a magana aikuwa bata bari antashiba tai karyar rashin lafiya kai kai tsaye gidansu rahma ta wuce bama tanan ta tafi islamiyya ganinta da uniform din nurses yasa ummansu kafin tai magana kodai khadija ce eh itace ainaga daga makarantama kike eh umma yaushe xata dawone kai aisai shiga towo gashi sauri nake ko akiratane a'a umma kyama fada mata daman ankuma kafe wasu sunayen harda ita kai Alhamdulillah ai yadda kikaxo ke xaki fada mata da kanki kinga vari na kira yayanta yaje ya kirata xasu barta. Tana xaune tana cin abincin da ummansu rahmar tatakura sai taci taji shigowarta umma lafiya daiko alafiya kalau kai harnaji dadi hankalina duk ya rashi yanxu nabaro gidan ace ana kirana bakuwa kikai towo bakuwa kuma wace kishiga mana kya gani tana shiga taga khadija sai murna aikuwa ta fada kanta yar duniya ashe baki manta dani ba haba ni na isa aibaxan manta dakeba suka dan taba hira kafin tace kinga bari natafi sauri nake wane irin sauri daga xuwa bakiga daga makaranta nakeba xuwa nai na fada miki ankafe mutun biyar harda ke ance ana nemanku gobe gobe kai dan Allah tafada tana ina xuwa ta fice dan fadama ummansu ai tafadan shi yasa nace akiraki da gudu tai bangaren yayanta. Har titi ta rakota kan gobe xasu hadu a sch. Data koma gida ta fadama ummanta itama tai murna sosai tace tamika murnarta ga rahmar. Karatu ya kankama duda an wuce rahma anman kasantuwarta tareda khadija yarinya mai kwaxo da san kharatu gata batada gyashi tadage sosai wajen koyama Rahmar sai gashi wanda ma aka fara dasu da dama tafisu. Rahma mutunce mai surutu ga jaye jayen kawaye hakan yasa tai suna sosai tasan mutane suma sun santa anacewa sai hali yaxo daya ake abota tanan dai xan iya cewa ba hakaba dan jininsu kawai ya hadu da khadija anman ta ko ina sun banbanta. Yanxu dan Allah kin kyauta kenan kawai kinsa naxama makaryaciyar dole kinsa nace bansan gidanku ba yanxu kuma sai kice nace masa ba'akafe dakeba inya ganki fa baxai ganniba xanyi duk yadda xanyi karya ganni haba kadija aikece sai kace mayya nace kidaina xuwa Aminu kano kinki harsaida kuka hadu naji yawwa ya batun jamb din haryanxu kinasan yi eh kuma inkikayi xakibar nan indai nasamu abinda nake so gaskiya xanbar nan wayyo xanyi missing dinki tai dariya suka cigaba da hirarsu... Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Af Rahma ban fada miki ba Allah ya amsa addu'ata ranar asabar xanyi jamb kinga baxanyi fashi ba kai anman natayaki murna ina suka kaiki cas ai bama sukaiki da nisaba eh wallah kinga da kina da waya ai da sai ki fadan result kan muxo sch uhum banni da batun wayar nan. Kinga yunwa nakeji dan xoki rakani na sayo rake wa to inbake ba da waxance gaskiya baxani ba kina kallo anjima mai family health xatai test ban iyaba karkije din ta fada tai ficewarta. Yawwa na sittin xaka yankan mai xaki ba tsoloba yai dariya kai gashi banida canji bata kudinta xan baka gaba daya suka juya inda sukajiyo muryar shikenan asirina ya tonu wannan mayen yagano ina makarantar nan yasakar mata murmushi tadan dauke idonta daga kallonsa a'ah nagode kabarshi Allah baxan baeshiba ba kyau maida hannun kyauta baya inji tsohuwar datake saida gurasa to shikenan iya xan karba danke tajuya nagode bata kara uffanba tai ciki. Tansan fadawa rahma but tasan intafada mata ta banu dan haka tai gum da bakinta malama ki aje karatunnan musha rake nace miki xan shane to kinsan baxakisha ba aida daxan tafi saiki fadanko yi hakuri duk na rikice ne Allah ban iya komai a wannan topic dinba nidai kixo musha bansan bayani nace banasha kawai inje ana test indinga tunowa da xakin rake nakasa rubutu Allah yashiryeki rahma in ana neman sarkin shirme anai meki eh naji ni yimin shuru kisha rakenki karta shigo. Hajiya kadija yau kuma kasuwar rake aka bude umar kenan insha xakai ai gwara kafada tunkan yajare waki banxa xansha saidai in va'abanba ni na isa inma rowa harkiyi yawa wai kuwa ina abba uhum abba yana nan ko jiya saida yace na gaidaki shine baka fadanba wato saidana ma tambayake ko ai yanxu xuwanda nai da niyar sanarki nai eh mana haka xaka ce am serious fa to naji kace ina amsawa yanxu kuwa yana ina abban shakali yana Germany kace abba anwaye lallaifa abvah anwaye aikece kinki rike waya da kina da ita ko dan charting dinnan akeyi ana gaisawa kayya barni da chart dinnan bata lokacine ke komai bata lokacine nura da yaxo wucewa inbakai sa'ama tace hirar da kukema bata lokaci bane tai dariya yanxu nura harda kai ko yai mamaki ashe tasan sunansa yatsaya suka dan taba hira kafin ya bar gun. Nayi xuciya da gorinnan naku xan dauko wayata haba ko kefa rahma ta dago ta fadi eyye yar gari wato daman kina jinmu inji umar tai dariya kudinne in akace xa'a biyemuku sai kubar mutun kubaro kuje ku hadidiyo littattafai mukuma ku hanamu namu yai dariya haka kika ce ko eh xan rama ne. Karubutan number din abba innaje gida nadauko wayar xan kirashi in hado datawa ya fada kajika kaida kullum ina ganinka eh anman sekin ga dama kike kulani ba sha'afa nake eh haka dama xaki ce. Abba shine mutun na farko cikin maxan sch din data saba dashi haka kawai takejin yaron aranta baxai wuce sa'anta ba inma tagirmeshi ko ya girmeta baifi taxarar shekara guda ba abba yarone mai faran faran da san jama'a ada bata shiga sabgarsa duda yakanxo susha shirmensu da rahma salonda yadauka yasa take shiga sabgarsa ita mutunce maisan xaman gaba sannan bata san kujera mai babararren baya dan haka take xuwa da wuri ta dau kujera ta sa'agaba in an fita break saita dawo taga gu wayam duda ta aje littattafai ahankula tagane mai daukewa ashe abbane ta fiskanta shi kuma salon nasa tsokanar a haka yake tun tana xuwa da muxurai ta karbo abarta harsuka saba yaxama kafin taxoma ya tarar musu ita da rahma danshi ba gwanin xaman gaba bane saboda baidan sch din waje yake dan fita. Lokacin da exam ta fito ma watansa guda a German duda kuwa hardashi awadanda suka ci. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Sannunku ta fada gami da tayar da sallarta Amina ce kawai tasamu damar cewa da ita yawwa yayinda yusra tace ni narasa me mutane sukeji insunyi girman kai zainab tace shi mutun badan kowan kowaba anman saiji daikai waishi mutum takamarsa yanada kokari da kyau kyan banxa kyan daba asali inji maryam Allahko ehmana ku vanda abinku kuntabajin inda mutu mai asali yake bearing sunan mum dinsa kumafa hakane da uba ake ado ahtoo kudaina damuwa dan anai muku girman kai mutum mai kashi a gindin suka saka dariya gaba daya tanajinsu tabidar da sallah dinta tashafa add'a tabar masallacin yawwa mujeko rahma suka bar sch din. Towo yau kuma bayero aka tuno kenan me kagani gani nai jaxo nan kai xamanka yaushe rabonda naganka anan ai tun muna bayero inmuxo practical kai dai barni inacikin tension name fa walkahi wata yarinya na hadu da ita cikin daliban nurses tayi mugun tafiya da tunani gashi duk yadda xanyi inyi taki fuskanta ta kai ko gidansu taki bani dama naje to saita baka dama kawai kaje watakil ma ganin bakaje ba yasanya take ganin wasa kake innasamu fuskar sanin gidan nasuba kawatta xaka samu tama kwatance itama kawar taki lallai naka wasane sai kace ba mubarak din dana saniba kaga malan inxaka ban shawara kawai kaban tobama nanba kana ganin maryam xata yarda kamata kishiya ka cika shirme wallahi karma ta yadda aini nake aurenta ba ita take aurena ba hakane fa maxa kasan me xakai ka aro mashin dan karka dauki motarka su bace maka kaje bakin gate din dasuke fita insun hau abin hawa kabusu ka gano gidansu give her a surprise visit nasanka ka iya love a hankula saidai kaga tana ni imba mubarak ba se rijiya suka sanya dariya. Shawarar nan takafa tayi malan wai maiyasa tun farko banyi wannan tunaninba hhhhh so ya tushe maka tunani kaifa kafiya shirme kaga nasan yanxu sun kusa fitowa toma mashin din waxan ara ka ari na masinjan ka kakuma kawo shawara. Yaiko sa'a bayan ansauke rahma har kofar gida aka sauke khadija yaji dadi sosai saida yadan jima a kofar gidan kafin yatafi dan vayasan ko banan ne gidanba tunda yasan yan makaranta kan biya aike saida ya cikawa haruwa tankinsa da mai kafin ya koma. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Wayyo gaskiya natayaki murna sosai wallahi nagode sosai nima yanxu yaushe xa'afara admission kai da saura kedai ki tayani addu'a Allah yasa subani to shikenan karki samu damuwa suka koma wata hirar yawwa na dauko wayata gata ki rubutan number dinki wow daman haka wayar take anman kike yawo kamar baki da ita uhum kedai bari inna dauketa ne ina tunawa da abubuwa da dama shiyasa ma ta fita a raina nidai gaskiya wayar nan taki tagama tafiya dani Allah ko eh mana kona bar mikine hhh khadija kenan wannan ta manyan yara ce dake ta dace ke manyan yara fa na nifin yan iskan jami'a ke kuma da fassara abu ba haka nake nufiba. Wai khadija taxo jeka kace tana xuwa wayyo umma dan Allah ni basai najeba kinga khadija bawai shawaraeki na nemaba umarni ne in kuma ban isaba to batasan batama ummanta rai dole tai abinda tace haka ta xari hijabi ta fice. Yana ganin fitowarta yaji wani dadi ransa dan yadauka baxata fitoba dake yana cikin mota bata kaiga fiskanto ko wayeba saida yaga tadan tsaya sannan ya bude ya fito aiko tana ganinsa ta hade rai yadan saki murmushi khadija ina yini akasan makoshi ta amsa kafin yafara bayani adan takaice ya mata bayanin kansa sunana mubarak mahfux gami da abinda ya kawoshi tadan kalleshi nagode sosai da nuna soyayyarka gareni saidan inaso kataimaka ka fiskanceni ada nataba soyayya saidai ayanxu babu ita atsarina dan Allah kabarni nagode ta juya xatai gida taku daya biyu taji muryarsa na fadin kitaimaka kiban dama xan xame miki farin cikin daxakiyi alfahari dashi xan goge miki dacin bakin cikin dawanda kikaso din yasanyaki tajuyo gamida murmusawa da'alama na bakin cikine uhum bakin ciki innace naxir yasanyani bakin ciki banma kaina adalciba soyayyace nace banai tai shigewarta gida oppp yafadai gami da dafe goshi dakyar yabar gurin yarasa meke damunsa. Lafiya kuwa naganki yau duk rai abace tadan dago ta kalleta ta cigaba da rubutunta batace komaiba haba kadija in wani abin nai miki basai ki fadanba anman ai baidace ba kixo kina ta wani kunbura nanma batace uffanba bakuma ta dagoba ta cigaba da abinda take haushi ya ishi rahma tako kwace biron kinga malama bansanfa wulakanci taya inai miki magana xakimun banxa au ke garkinsan wulakanci ba dadi kikaimun me nai miki ta koma ta xauna sai hawaye ganin haka yasa rahma komawa itama taxauna kifadan me naimiki xaman tare bashine karike mutun ranka dan yai maka laifiba. Yanxi rahma kin kyauta kenan da kika fadama wannan mutumin gidanmu ta dafe girji ni khadija wallahi bani bace to waye inbakeba ke kadai kikasan gidanmu haba khadija ki yarda dani mana wallahi bani bace ki taya xandinga rantse miki kan karya dan kawai inasan xama dake kijedai kiyi bin cike ta mike tabar gurin. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Mikewa tai tabi inda Rahmar tai tadan dafata nayarda rahma ko baki rantseba nayarda tai murmushin yake Allah baki yarda ba tunda ai dana ce bani bace cewa kikai ni daya nasan gidanku naji bakeba ce nakuma yarda wallahi tagaske Allah toma wai yaushe yaxo ranar juma'a tabata labarin yadda sukai gaskiya baki kyautaba aida kinbishi ahankula kinji maixaice da tun asannan xakigi yadda yasan gidanku kufa hakane anman dai ya wuce ko tai dariya suka mike suka koma inda khadijar ke rubutu. Yadda mubarak ya takura da xuwa nacin yau daban nagobe daban yasanya tun bata bashi fuska har tadan saki jiki dashi duda ita har lokacin batajin xata soshi koda dawasane kawai dai tana girmamashi fuskantar datai yanada mutunci. Gaskiya xanyi missing dinki wallahi yanxu shikenan kin barmu uhum Rahma kenan ai xumuncin mu insha Allahu har a aljannah baxai tsaya ananba duk wanda suke gaisawa a sch din tai masa sallama masu tayata murna nayi masu kushew nayi dayake ita takeso bata wani damu da kushewarsu ba xoki rakani gun malamar anatomy inmata sallama dayake suna dasawa da ita yanxu kin kyauta kenan khadija dakinsan baxaki dore ananba ai dabaki fara xuwa ba dakin barma masu so sun naima yanxu kinga babu damar asa wani kunyi nisa da yawa tadan murmusa kafin tace wallahi mlm ba lefina bane daga gidane sukasa na raba kafa koda baxan samu daya va sai in daya to yayi kyau Allah ya bada sa'a tace amin suka taso suba fito yanxu yaushe xaku fara karatu Monday dabadan da sch ba ai danaxo muje tare inji rahma hhh ai xaki iya. Mai sunan manya na'am abba yaushe xaku fara exam ne da saura sosaima saidai wasu na attendance kuma shima da yar matsala in baka sameshi ba towo kace baxamu dake ba abba ina xaku mubaraka ta haihu lah abba yaushe yanxunnan muka gama waya da mijinta yake fadan ne tahaifa mace ta haifa gaskiya nidai xani ace diya guda baxanje ganinta va aisaita xata ba uwar gaske bace aikodai baxakiba nagama mgn da maman naxir xakije can tunda canma kamar gidane kixauna kafin mudawo banasan daga farawarku kifara samun matsala kinji ko to abba. Yanxu yaya baxaki xoba kenan haba kanwis ba lefina bane abbane yace inyi hakuri sabida sch toshikenan yaushe xakixo semunyi hutu xuwan musanman xanyi to aikece kodam chat dinnan vakyai da aikinga baby din kibari xansa nafisa ta buden inyaso naga diyata yawwa yayamur yanxu kuna asibitine eh basu sallamemu ba to Allah ya karo lpy ya raya mana ita amin yaya eh lallai wato ko yar kunyarnan babu tai dariya to yaya kefa yayatace keda xakixo kina kusa dani in ance Allah ya raya kice amin bakyanan basai na wakilceki ba aikon ya kamata . Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Mama ina kwana lpy lau kadija badai harkin shiryaba na shirya ina sauri munada lecture din safe to kitsaya ki karya na makara yanxu bakwai da kwata aiko sai kinci abinci xaki tafi tadan murmusa mama malamin yanada tsauri inyashiga ba mai shiga to ki diba inkinje can kyaci to mama waccan kasar bata tashiba ko eh tace yau basu da lecture ne barta ko tanada ba lallai ta tashi yanxuba tafiya san bacci kije nace bala yakaiki to mama sai nadawo Allah ya bada sa'a ta'amsa da amin ta fice. Sun futo daga lecture a agajiye gashi duk yunwa ta isheta khadija xomuje kafteriya yunwa nakeji wlh gashi lecture dinma bawani ganewa naiba naxo da abinci xo muci inbe ishemuba maje mu kara sunaci suna hira. Wayarta tai kara taduba mubarak ne tadanyi murmushi tasan korafine yaje gida basanan takara wayar kunnenta ya amsa akagare kin kyauta kenan danai mai aikin fini sani dan Allah kafadan kika bar makaranta baki fadanba naje gidanku akace kunyi tafiya tai dariya maida wukar nadauka na fada maka wallahi tafiya kuma vani aka tafi ina nan ynxu ma ina sch haba kadija bansanki da karyaba gani a sch din rahma tacemun kinfi wata da daina xuwa sabida bakidauken da mahinmanci ba shine baki fadanba kayi hakuri xance ne bai kawo xance ba ai girmankine na hakura nagode ta fadi suka dan taba hira kafin su aje wayar. Umma dakanta bayan sun dawo taje taima mama godiya tadauko khadija suka dawo gida. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Yan kwanakinnan mubarak bashi da aiki sai takurama khadija kan yanasan tabashi dama ya fito so yake tayi karatunta agidansa kememe taki dan batasan tashin hankali duda bawani san mubarak takeba. Yanxu kana ganin iyayenka xasu yadda ka aureni yai murmushi to mai yasa baxasu yarda ba na fada musu komai nixan xauna dake basuba to aishikenan xan fadama abvana dagaske kike na taba maka irin wannan wasanne yai murmushi bari na wuce yau inada aikin dare sukai sallama. Koda ta koma gida take fadawa umma yadda sukai taji dadi sosai dan ayanxu tunda ya rage shekaru biyu kadijan ta hada karatunta take fatan Allah ya fito mata da miji tai aure dan da'ace sch of nursing dince da tuni tana aiki tunda ga rahma tana aiki tayi aurenta har da ciki. Biki ya rage sauran satittika ita dai amarya ta rasa farin ciki take ko bakin ciki maman nasir da ita ake komai taxage da aljihunta da jikinta hidima kawai take duk wani gyara da yakamata ta wakilci umman khadijan ita take mata. Yau khadijan suna da lecture yakaisu har magariba agajiye ta dawo ta tarae da mama ita take jira tanasan ta tafida ita xata kaita gurin gyara saida taci abinci mamar tai sallah sukaima umma sallama har sun shiga mota tace af namanta littattafaina kinga sai in wuce sch gobe daga nan yisauri kinga munyi yanma mama tana kallonsu suka faka motar bata kawo komai rantaba xatonta kawayen khadijane ko yan uwansu dasauri khadija ta fito yawwa ga minafukar nan sukaji anafadi lafiya tafada sai jitai anbata mari ke banda tsaurin ido naki gaki shegiya kice mijina xaki aura ai ba lefinta bane anti lefin yayane da ya boye mana bawani lefinsa rufarsa sukai xasu bashi ita matsayin mai asali wata motar ta sake tsayawa aiko suma kungiyace guda suka hau taken nasu bala'in da sauri mama taxo gaba kukuw bayin Allah mai tai muku kawai xaku hau dukanta wata cikinsu tace watakilmafa itace munafikar karuwar uwar eh nice nahaifeta mexakumun eh lallai tunda kun asircemin miji xaku vashi shegiya va kodayake ba lefin kubane wallahi mubarak ya cuceni inma kishiyar xaimin anma yarasa damai xaimin saida mara asali aiwa wannan xubda mitincine ta fashe da kuka ita dai kadija tunda ta dunkushema marin da akai mata tafara hawaye bata kara cewa kanxil ba umma najin hayaniya ta futo sukai kanta da fada harsuna kokarin dukanta mamace takira police dakyar suka sa sukabar gurin batajira shawarar umma kota khadija ba ta kira mijin safiyya yaxo dashi da kaninsa tasa suka devi kayan lefen da'aka kawo da duk wani kayan aure tace amaida gidansu mubarak aure baxa'a vashi ba saida ta gama da wannan sannan ta kama hannun khadija tasa amota takamo umma suka shiga ciki kiyi hakuri da'abind sukai miki jahilci ke damunsu watarana xasu gane maganar aure karki damu baxa'a fasaba randa akasaka ranar xa'a daura anman bada dansu ba da wanda xaiga mutuncin khadija ta riketa ayanda take yasota haka yadda take bata jira maganar ko amsar ummaba tai ficewarta daga gidan....... Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Tunda suka ja motar khadija ke kuka mama na kallonta bata ce uffanba bakuma tace tai shiruba dan tasan kukama kan ragema mutun bakin cikin dayake ciki saida ta bari tai mai isarta kafin tafara rarrashinta. Wani abu dake bama khadija mamaki anfasa biki to maye sai subje gurin gyaran jikin itakam nabayama yavisheta anman kamarma an xuga mamar yin abinta take ba kama hannun yaro gashi khadijar najin kunyar tace abatshi. Yau rukayya bataxo sch ba khadija naxaune ta jiran time yayi su shiga lecture zan iya xama taji muryarsa kamar daga sama ko ba'a fada mataba ta gane muryar mubarak ne dan haka ta mike tsam batare da ta ko kalleshiba xatabar gurin dan Allah khadija kitsaya kisaurareni najejje gidan dakike anhanani ganinki yanxu kema kice baxaki saurarenba ya kikesan naida rayuwata kimin adalci mana ta juyo afusace uhumm lallai bakinka yake furta adalci kai kamun adalcin katuro danginka suka cimin mutunci sukaci xarafin iyayena haba khadija yaxaki dinga cewa na turosi saninkine bananan banma san anyi hakaba saida na dawo ohoo nasani kona ba inda xaka kacemin xakai tafiya dan kafasa aurene mene saika turo anci mutuncina aiko ni kafadawa xan fahinta dan Allah kadija kidaina cewa ni naturosu kimin adalci pls. Kayaudareni kayaudari iyayena kamin karya kace iyayenja sunsanni ko wace ashe bama kaje musu daxancenba duk dadewarmu dakai baka taba cemun kana da mataba saigata agidannu taya kake tunanin xan fiskanceka ayanxu vacin kagama tabbatarma da xuciyata kai makaryaci nasani kadija nai kuskure da yawa kiyi hakuri ki sauraren uhumm aini ba'abinda xaka fadan Allah tasoni da basaida aka daura nashiga matsalaba inaso kasa aranka ni khadija koda ya rage dagani saikai aduniya Wallahi gara na mutu ba aure dana aureka kaje kanaimi yar asali kama matarka kishi dan gudun xubewar darajarta fuuu tabar gun yabiyota da sauri yana kiran sunanta taja ta tsaya kaga malan ina anmaida ma da kayanka inkuma akwai wani kafadan sai abiya anman kadaina bina inba hakaba wallahi a sch dinnan xan yagama rigar mutunci danni daman kasan ba ita gareniba ta bar gun ya dafe goshi maryam tariga ta gama cutarsa.... Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Wani abu da khadija bata fuskanta ba shine yadda taga gidansu ya cika da yan uwa duk su mubaraka anxo gidan gidan mamar ma duk ancika batasan meke faruwaba itadai takanje makaranta ta dawo asha hira saka makon gidansu babu dadi xaman sabida yadda bakin ke hantararta yasa ta dawo gidan mama da xama mai kitso da filawa na musanman aka dauko suka mata yakara fito da ita sosai ta tambayi mama tace bikinne ake bata kara daga nanba dan haka taci gaba da sabgarta. Kamar daga sama taji ana tashinta tadan bude ido taga rahma ce tsaye da katon cikinta tai tsaki ta juya taji ankara tabata taga bilkisu towo yau kuma mafarkin kawaye nake taja bargo wai danta kara jin dadin baccin aiko bilki ta janyo bargon dallah malama tashi xumbur ta mike dan tagano bawai mafarki takeba tasa ihoo yaukamar kun hada baki da sassafennan saiga Aisha ta shigo rike da les a hannunta wayyo wai dagaske ba bacci nakeba watakil baccin kike lokacin da Fatima ta shigo ta fadi haka wai ace amarya guda har goma tana sharar barci ko wanka bataiba amarya kuma mu suka basar ke yanxu haka ake tarar baki immu kina ganinmu Aisha fa yau kimanin shekaru biyar ba'a haduba anman baxaki tashi ki mata oyoyoba kyale mara mutunci inji rahma maxa mike nakai miki ruwa kiyi wanka ta saki vaki tana kallonsu tana wankan tana tunanin meyasa sukaxo atare haka. Muryoyin datake jiyowa yakara sata hanxartawa ta fito su rukayyane da wasu course mate dinta na bayero kwalliya kam tashata tai kyau sosai ta fito amaryarta sosai ita kanta tasan tai kyau duda ranta ba dadi abinda yan uwan muvarak suka ma ummanta na ranta anman yadda taga kawanta har wanda ta manta dasu nata xuwa anata cafta kamar a sch yasa ta ware taketa warkajaminta itama. Ke abinki dagwas in an daura aure basai ankaikiba tunda gaki gidansu ango tadan kalli Maimuna kamar yafa suka sheke da dariya xaki gane ne kunga bari naje nagaida mama na dawo ko najiyo dadlilin wannan taro haka auke saida dalili xamu kawo miki xiyara ta fice batare da basu amsaba. Yadda taga gidan dankam yakara bata tabbacin da dalilin wanban taro kamar daga sama taji maroka na fadin Alhamdulillahi an daura auren kadijatu da angonta jafaru bata kara yadda ba saida taga anata faman fadin amarsu amarya bakya lefi saima yanxu ta tuna yaunefa ranar da tai dai dai da ranat da'aka sanya ta daurin aurenta da mubarak. Kafin kace mene maxan daurin aure sun cika gida anata hotuna abinda yabata mamaki yan class dinsu da dama sunxo na buk su umarma duk sunzo na nursing gaskiya da'ace tanasan bikinnan datayi farin cikin yadda aka mata kara saida maxa suka dan watse umar yaxo suka gaisa yabata wata leda inji abba yaso xuwa suna exam ne daurewa kawai take dan kadan take jira ta fashe da kuka fuskantar hakan yasa bilkisu janta xuwa daki aikuwa suna shiga ta fashe da kuka saida tai mai isarta sannan bilki tai ta mata nasiha dakyar tasamu tasha kanta tasa tasake wanka takira rukayya tasake mata kwalliya tafito fes tai kyau abinta baxaka taba cewa tai kuka ba. Ita dai tasan batai gayyaba anman yadda taga kawayenta yabata mamaki tasan bakowa keda wannan aikinba sai rahma bilki da rukayya itakam ba'abinda xata cemusu sun mata halacci dan dabadansu ba bikinma balallai ayishi cikin kwanciyar hankaliba dan yadda inta tuna mijinma sau biyu suka taba haduwa shima bada sunan soyayya va yadda taji ana fade benasan da batun aurenba se jiya itako wane irin aure aka mata wane irin xama xatai da addu'aba. Haka nake sanki F.A.Ya'u Da yanma yan uwansu sunxo gidan tai mamakin ganin yan uwan ummanta takumaji dadi sosai burinta yakusa cika tunda gashi dalilin bikinta har yan uwan ummanta da suka jima da rabuwa sunxo cika kam ancika sosai burinta yadda haihuwarta ta cire ummanta daga dangi haka take san taxama sanadiyar maida ummanta abarso ga yan uwanta. Washe gari kayatacciyar dinner aka hada duk wanda yasamu xuwa yanada tsarabar smart phone da atampa biki kam ya kayatu ango kawai yai masa cikas sakamakon yana da karashen abubuwan da zaiyi yasa sai wani watan xai dawo. Ranar lahadi takoma gidansu dan ummanta acan xatai yininta nanma biki akai na alfarma gidansu ba masaks tsinke amarya amakota tai taronta da daddare aka kai amarya gidanta dake sultan road gidane da yagaji da haduwa tsayawa bani bata lokacine kowa ya watse sauran ita dasu bilkisu ra rungumesu tana kuka gami da godiya kunmin abinda kun wuce kawaye kunxama yan uwa bani da bakin gode muku ko kadan bilki tadan dagota dalla mu kimana shiru ance miki dan kigode mukayi ai kin wuce nan wallahi wai ya'akai kuka san da bikin kinsan safiyya duk tasanmu tasan gidajenmu nida rahma taxo ta samemu ita da mama suka fada mana sunasan mugayyato kawayenmu dan ba'afasa biki ba kinsan kin fada mana anfasa nadau nauyin gayyato na secondry dana islamiyya rahma tagayyato na nursing tace xata samu rukayya ta bata kati ta gayyato duk wanda tasan kuna gaisawa a bayaro tabkalli rukayya wato ke kinsan da vatun baki fadanba ko tai dariya ai ance yaxama sirri suka saka dariya safiyya ce taxo lokacin da kowacce mijinta yaxo daukanta sukai sallama cikin kewar juna. Mamace tace naxo natawo dake sabida jafar sai nanda wata guda xai dawo batasan barinki ke kadai cikin gidannan hankalinta vaxai kwanta ba tai dariya mama kenan bata gajiya suka tawo. Yau umman khadija tafi kowa farin ciki domin ita da kanta taima diyarta nasiha tasata motarda xa'akaita dakin mijinta mexatama Alkah inba godiyaba. Khadija kwance kangadonta na gidan mama ta xurfafa tunani tabbas ko jafar baisanta xata xauna dashi kodan karamcin family dinsu xata daure ta xije duk rintsi bayan ummanta da abbanta da basir dinta sai bilki da rahma vataga wanda ya nuna mata kaunar da mamansu jafar taimata va tayadda nazir ba mijinta anman haduwa dashi aikairi ne ga rayuwarta komai taxana sanadiyarsa ne komai tasamu sanadiyarsa ne baxata taba mantawa dashiba baxata taba dena masa addu'aba. Haka nake sank Na F.A.Ya'u. Sanye take da ruwan hanta tai mata kyau sosai ta yafa mayafinta shima kalar rigar sai takalminta mara nauyi rike da jakarta wadda daga inda kake xakaga abinda ke ciki itama tadau dige digen kayan takyau sosai ta fito mama ni xan wuce to sai kin dawo af ban fada mikiba jiya jafar yadawo shima nace yakaiki tadan kalli mamar taga ba ita ma take kalloba to mama yana ina yanxunnan yafita tace kisameshi a mota yawwa mama xan biya ta gidan bilki haba khadija daga aure sai yawo kibari ki kara lokaci danma illimi illimine ai da ba inda xaki dinga xuwa to mama sai nadawo Allah ya bada sa'a tafice. Tunda ta fito idonsa na kanta har yakasa daukewa yarinyar nan mekyauce ya fada a hankula mama bata kyautaminba datamin aure nasan kowace xata auran baxatakai khadijaba yadanyi tsaki tariga karyan tsari banda tsarin mata biyu but dolema na auri kadija kowa ta auramin danna fiskanci tanasan matar data auran dan yanxuma da yaje gaisheta tamai maganar amarya yafara kunkuni tai xuciya tace ya fita yaba guri. Baima tsaya yaji wace amaryar tasa ba ahankula ta bude motar gami da sallama yah jafar ina kwana baxan amsaba tunda bakixo mun sannu da xuwaba wallahi bansan kadoba amin afuwa toshikenan anmiki suna tafe yana janta da hira sama sama take amsa masa yanxu sauran shekara nawane karatun naku shekara daya da watanni masha Allah gaskiya kunyi sauri nikam naga dadewarmu duk nagaji wallahi yai dariya haka karatu yake kuma xakiyi aiki inkin gama tadanyi shiru na cika magana ko tai dariya sai hakuri to yanxu aurefa yaushe xakiya tadago dasauri ta kalleshi sai na gama ok bakyasan hada karatu fa aure ko eh da wuyane sosai ma tace inda yai dai dai da tsayawarsu inda xata sauka tama godiya ta wuce. Tun da taxauna take tunanin hirarsu watoma baisan ita matarsa bace ko ya raina mata hankali ne. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Tun daga wannan ranar jafar ke jakaita sch ya daukota komai yaso natane koda yadauko jakarsa tsabarta tafi ta kowa yawa koda hajiya tace ina na matarsa cewa yai se daya jakar taxo tai dariya kawai dan tafiskanci inda yadosa aurenne beso khadija yake so tace dani kake xance. Yau bayan ya kai khadija sch ya biya ta gidan kanwarsa safiyya tare da tsarabarta tai murna sosai kafin kace mene ancika masa gaba da kayan kwalama saida yaci yasha suka dan taba hira kafin safiyya tace yaya wai yaushe khadija xata tarene wacce khadija kenan khafini saninta Allah ban saniba khadijan yaya nasir mana what ya fada gami da mikewa tadauka ko kishine na kiran matarsa da sunan wani hi hakuri yaya vansan na batama ba no no wai daman khadija nada aure tadan kalleshi gami da shekewa da dariya lallai yaya wai daman bakasan itace matar ba me kikace ta mike tadauko aibin bikin ta nuna masa yakaranta sunansa ne tadaiko jaka shine da khadija jagwab yaxauna na kwafsa yaya mekayi yabata labarin yadda suke da mama kan amaryarsa lallai yaya ka kwafsa keni barni naji da kunyar data isheni bansan daya xan kalli umma da khadija va. Ya tafiya safiyya ta kira umma ta fada mata yadda sukai dashi tai dariya ai nadade da ganoshi santa yake baisanma tasa bace xan maganinsa. Kai tsaye gida ya wuce bayan yaci abinci yasamu mama suka gaisa kamar vatasan ya sukai da safiyya va yaxauna yanata xuba mata hira so yake tai maganar amarya taki ita kuma dayaga baxatai ba yace tawwa mama yaushe amaryar xata tare talleshi sheke ke wacce amarya mata ta mana au daman kana da mata yai saurin kallonta aini bansan kana da mataba in kuma wadda na aurama ce ai nafasa jira nake daman kaxo kabama yar mutane takardarta haba mama nifa bantaba cewa bansanta va eh bakace ba anman aika nuna ko inkula dan Allah mama kiyi hakuri Allah insan mata ta nikaga tashi kaban wuri. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Sin sin ya fice daga dakin kai tsaye sch ya wuce dan dauko khadija bai wani jima ba ta fito lah yaya jafar ashe har kaxo yadanyi murmushi eh ke nake jira suka wuce. Harkin dawo eh mama dake yah jafar ya kawoni au saida yaje kince karyaje jeki kici abinci naga agajiye kike ta wuce daki. Yawwa na kiraka ne inasan daga yau karka sake daukarmin diya xuwa koma inane xan sami maikaita hajiya sabida me sabida nace ka saketa kaki dan Allah hajiya kiyi hakuri akasi aka samu ada kasani bana mgn biyu dan haka indai har baxaka xo min da maganar sakin yarinyar nanbq inasa kadena min maganarta kaji ko. Duk yadda jafar yaso sha kan hajiya abin yaci tura dan kamar kara tunxura ta ma yake gashi ta hanashi ganin khadijar inyaxo falon inxeyi awa nawa baxai ga khadijanba makarantarma besan lokqcin datake tafiya ba. Yau kam ko aiki yace baxai jeba sai yaga khadija duk yadda xai seyai yasa tacema hajiya akaita gidanta duda itama yarinyar bata taba nuna masa shidin mijin tane ba Yana farfajiyar gidan gindin bishiyar mangwaro ya hangota tana fitowa tai kyau sosai wani kishi ya rufeshi ace matarsa ce xata makaranta cikin wannan adon duda ba shigar banxa taiba yama manta da abinda yaxaunar dashi afusace ya mike yai inda take tana ganinsa ta fadada murmushinta yah jafar ina kwana be amsaba yahau fada yanxu wannan wane irin abu ne xaki sch kinsan da maxa anman xakiyi kwalliya haka yah maine aibin wannan shigar haka ma xakice dan kin rainani to wallahi inkinga kin fita to saikin sauya kayannan shigar tai murmushi batace komaiba ta koma ciki mama na kallonta ta shige daki bakar riga ta sako sai hijabinta iya gwiwa Golding kalar adon rigar sai takalminta shima golding tai kyau koda ta fito mama tace sekin makara ko wadancan ne naga sunmin wani iri koda yaganta gani yai ta kara kyau fiye da daxin yai tsaki kawai ko basuyi bane suna a'a sai kin dawo tana fita yashiga gidan yana kunbure kunbure kai kuna lpy dan Allah mama kina kallon yarinyar nan take kwalliya wajen xuwa sch eh lallai daman kai kasa taxo sauya kaya aida ta fadan wallahi baxata sauyaba. Abin duniya duk ya ishi jafar dan haka ya yanke shawarar xuwa yasamu yayan babansu yasanar masa mai makon yace wani abu sai dariya kawai yai jafar kenan watakil basu gama shirinsu na mata bane tunda kaga ai auren ba shiri akai ka kara basu time. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Abu kamar wasa karamar mgn ta xama babba dan jafar ko aiki ya dena xuwa duk ya fada tun mama bata damuba harta yake shawar gwara tabashi matarsa karya cutu. Iya shiri da gyara duda wanda khadijan tasha baya haka mama tai mata bilkisu da safiyya sai matan abokin jafar biyu da maxajensu bayan yayar mama taxo tadauki khadijan suka tadda agidan saida inna ta dawo sannan mama ta shiga bangaren jafar din yana xaune saman kujera idonsa arufe tadan tabashi ya bude ido mama kece eh nice takalli gebensa kwanukan abincin datasa akawo masane da'alama ko kallonsu beba balle yaci yanxu kai haka xaka xauna baxaka ci komaiba banajin yunwar ne ai shikenan xuwanai naga ganin kadija dakake ke kara hanaka yin abinda nace nasa duk kayanka an diya ankai gidanka na sultan inaso kai wanka kaxo kakoma can ko kasamu ka war ware yadan kalli mama baice komai ba be kuma motsaba wai badakai nakeba ne ya mike yashiga bayi jika jikarsa kawai yai yafito ko mai bai shafaba ya xura kayansa yarasa me yasa mama takasa fuskantarsa ko ganin halin dayake ciki batai sema korarsa daxatai har ya kai kofa dauke da jakarsa yaji tace kamanta vaka karbi mukullinba ta mike taxo dab dashi ta danka masa yakarba Allah ya karo sauki yace amin mama aransa yana cewar komai xa'ai wallahi baxai saki matarsaba. Yajima a cikin mota koda ya shiga far fajiyar gidan nasa kafin yashiga gidan yana budewa salim da abbakar sukaxo tararsa yai mamaki to sukuma wadannan yaushe suka shigo wama ya bude musu tunda dai shi yasan mukulli nagunsa ango ango wato saima yanxu kaga damar xuwa ka shirgamu ko yadanyi tsaki wane ango anhashi amarya suka saka dariya salim ya jashi xuwa falon safiyya ta taso yaxaku shigo dashi ba vayani aiko da sauri tai dakin da dja ta shiya yanxunnan ta kullo ta dawo inda suke ai inkunga yaga amaryar nan to kuwa mun kayyade ciniki aikodai se an biya kudin baki inji matar salim anji nawa kuka mata kudi bilkisu tace kunsan amaryar tamu tadabance dan haka dole abiyamu da tsada kufa matsalane matannan kunfiya san kudi inji abbakar inbaku biyaba sai mudau abarmu mutafi hakadai kudi kudi to kaji ango ni kunga ko nawane kubasu kuhada matanku kubarmin gida iyye haka ma xakace wallahi kai wasa semu kwana nan what aiko da kare xan sanya yai waje daku suka saka dariya. Yar karamar walima suka hadama ango da amarya ta kayatar sosai wajen takwas suka bar gidan yaxama daga ango sai amarya bayan ya rufo kofar gidanne ya tsaya yana godema Allah wai yaushine gida daya da khadijansa yasani mama ta gama masa komai baida kamarta. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Tana xaune kamar yadda ya xata yai sallama ta amsa masa asanyaye har ka dawo eh wallahi yadan xauna kusa da ita khadija ya fada ta dago ta kalleshi kafin ta dauke idonta bakiyi farin cikiba ko dame da aurena tai shiru nasani mamace ta takura miki ko tai shuru nasa me kike tunani me nake tunani tace ki tunanin an min auren dole ko an aura min ke bana sanki ko tai saurin kallonsa kamar yasan hakan take tunani yai murmushi na canka inasan kisa aranki kasan tuwar bamuyi soyayya va kasantuwar bansan da batun aurenmu ba kasantuwar ban taba cewa inasanki ba bashi yake nufin ban sanki ba tun bayan rasuwar kanina nake tausayinki ban gano na kamu da sanki ba saida na koma lokacin dana gano kedin mama ta auramin nai farin ciki farin cikin daban taba yiba arayuwata kisa aranki ni maisanki ne xankuma soki har rayuwata aduk tsanani karki sanya asalinki a matsalarmu hakan bai xama komai ba gare ni takalleshi dagaske kana sona inasanki nasan nan gaba xaki yadda da haka. Khadija kam tasani tai sa'ar miji mai santa mai kula da ita duk inda ta motsa yana biye da ita makaranta adole yake barinta gun aiki dakyar yake iya fita itakam ba abinda xata ce sai alhamdilillah burinta ayanxu bai wuce dai daita ummanta da kakanta va fuskantar hakan yasanya jafar yadaiki aniyar tayata cimma burinta. Tun bayan rasuwar matar malan tukur lokacin baxa wuce aji biyu a primary ba rabonta da unguwar yakasai yau ta gudiri niyyar xataje komai xa'a mata kuwa sai taje. Adai dai kofar gidan ta parker motarta yana xaune kamar yadda yasaba xama bai kawo komaiba game da motar ta sauko ya bita da ido bai fiskance taba taxo gefen tabarmar da yame xaune taxauna abinda ya kara bashi mamaki kenan tagaishe shi ya amsa fuska ba yabo ba fallasa baba baka gane niba ko eh kimim karin haske tai murmushi kafin tace dan Allah baba kamin alkawarin komai baxo ma dashi vaxaka koreni ba yai dariya inbaifi karfin hankalina va nan tafara masa bayanin kanta kafin daga karshe tace nice khadijar jikarka ta wajen saliha da mamakinta taga ya fadada murmushinsa yarinya kifadan gaskiya wallahi baba da gaske nake yanxu to ina ita uwattaki ki tai maka kikaini gunta inasan naganka ta yafemin konasamu sassauci ga abinda nai mata ita da babarta itama ta mike kaya hakuri baba batasan baxo ba xan kawota ita yakamata taxo bakaiba yaja hannunta sukai cikin gidan daki daki ya nunata duk inda sukaje sai tamusu alkairi bayan sun fito tasa aka sauke kayan data yo musu tsaraba. Umma kimin afuwa nai miki wani laifi kadija ta fada maisunan manya komai kikai min na yafe miki umma naje gun abbanki me kikaje gunsa mutumin daya koreni akan naki kaahe ki haba umma kiji tausayinsa mana mahaufine fa kema kin haifa inji abban khadijan da ya shigo yanxu kiyi tunanin halin daxaki shiga in akace yau khadija ko su mubaraka sun haifi da va aure shima fa haka yaji anji yai kuskure anman bakiga yadda yake san ganinki ba ba tun yauba duk inda yasan xai ganni xuwa yake kanna kawo shi inda kike naki kace kawai kana bin bayansa wato gori xaka min ko haba saliha aikinsan ko labari aka baki nayi miki gori kyace karyane ai gwanda sakace lbr ynx agaba na kayi fuuu tabar dakin khadija ta durgushe tana kuka. Shiko tsohon tun xuwan khadijan yake xuba idon yaga dawowarta anman shiru gashi har andoshi sati har ya cire ran dawowarta katsam yana xaune adakinsa yaji talatu na buga salati saliha dagaske ke nake gani da hanxari ya fito ita dince aiko kan kace me wannan duk matan gidan an fito yajata daki khadijan ma anan yabarta sauran matan nata kallonta ita kuka shi kuka dakyar yai shiru yafara neman afuwarta haba baba nice da lefi ni ya kamata na rokeka afuwa nima ban kyauta ba na yanke xumuncinki da yan uwanki ni baba tuni na yafe maka fatana ka yafemin kadawo dani matsayina na da nadade da dawo dake nadade da gano kuskurena. Kadija kam tafi kowa farin ciki ganin yadda ummanta taketa nishadinta cikin yan uwanta itama kanta datai shiru xa asata cikin hirar duk sansu nasasu farin ciki su harira da kuka suka dinga rokon umman gafara kan abinda sukai mata. Kwanci tashi ba wuya yauce ranar farin ciki gun dja domin yau ake yayesu a sch dan sun gama service dinsu ta fita da result mai kyau wato first class su biyar ne a course dinsu duk maxa ita ce kawai mace se masu second class upper da yawa burinta ya cika duda kuwa ita ba abinda take so sama da akirata prop. Tasani inda rai wataran shima mai cikane. Ummanta ce ta saida gidanta da filinta ta bata gashinan burina nayi makarantar lpy ko karatu kan lpy na bude pharmacy ashe diyata na cima burin nasani inkin bude ko bayan raina baxakiyi kuka kan rashin abinda xai rikeki ba koda kuwa baxakiyi aikiba ta rungume umman tana kuka tana godiya tasani ummanta tafi karfin uwa kawai saidai uwa da uba dan wani uban vaxai yi abinda take mata ba koda tajema da jafar da batun yafi kowa farin ciki danshi daman bayaso tai aiki shine ya shige mata gaba kan komai inda ta bude katon pharmacy dinta. Kafin kace mene har ta bude wasu branches din bakuma wai kanana ba harsun fi na farko magani kuwa duk tsadarsa kasameshi a gunta. Shekaraesu uku da aure khadija tasamu ciki murna gurin jafar ai ba'a mgn aranda yasamu labarin cukin ai duk wanda yasanshi yasan da cikin kai kace har anyi haihuwar dan yaxuma in khadija batace dadyn baby ba bama tako kallonta.nakasa Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Khadija tasani duk wani farin ciki da mace ke nai ma ta sameshi abu daya ya rage mata cikin burinta shine tanasan ganin babanta na asali tanasan kosau daya ne yace yanasanta koda kuwa baxai karbeta matsayin diya va tanasan kosau dayane yau ace itama taga yan uwa daga ban garensa yau ta dauri aniyar komai wuya konai rintsi xataje ta tunkari ummanta da batun abban nata. Umman na tsakar gida tana wanke wanke khadijan tashigo vayan sun gaisa ne tace umma yanaga kina wanke wanke ina binton tai dariya aini da kuka kawota naga antauyeta ace yarinya karama anbarta se aikatau shi yasa nasanyata a makaranta yanxu tana can umma kenan basai ki bari ta dawoba banda abinki intadawo abinci xataci ta tafi islamiyya intadawo ta gaji tana aiki anman se alhamin juma'a da asabar da lahdi umma kenan kawo na wanke basshi kiji da cikin nan ace haihuwa ko yau ko gobe mutun yana yawo tai dariya umma kenan kigama gurin ki naxo ai nagama ta fada tadauke kwanukan tai kicin taso mushiga ciki. Suk kara gaisawa kafin khadija tace umma daman xuwa nai kitai maka ki fadan inxa xan samu babana ko wani nasa xumbir ta mike kina haukane ko asharia baki da uba nice komai taki kima cire aranki kinada uba kinji ko khadija tasa kuka ummana dan Allah ki tai maka ko daba xaki yafe masa ba ni kimin ixinin xuwa inda yake na miki alkawari baxan taba cewa kimai a fuwaba umma ki taimaka kodan kar awratayya ta shiga tsakani inda be halattaba ina ruwana tama shiga shine da hakki duk yadda khadija taso umma ta fahinta taki. Gun abban umman taje tasameshi har gida yaxo yaita mata nasiha dakyar ta yaddarma kadija taje kan sharadin baxata taba kawo mata mansur neman afuwa ba. Misalin karfe hudu jafar ya sauketa a kofar gidan gidane babba a kofar gidan ya tsaya tashiga yadda taga gidan batai xaton da mutane ciki ba dashi da kango duk daya tai kamar baxata shiga ba ta daure ta karasa taje daf da falon tajiyo kamar hayaniya dan haka ta kusta ta shiga wani ta gani kwance da alama baida lpy sai wata budurwa baxa wuce shekara ashirin da daya ba tana tsaye kansa tana fadin kaga baba ni ba ciyarni kake ba babu ta yadda xa'ai kace xaka hani abinda nake so bataji mai yace ba taji yarinyar na fadin dan kai haifeni sai akace naxama baiwarka ni na dora ma cutar fuuu tayo waje xata fice taci karo da khadijar ba khadijarba harma ita fiddausin saida taja ta tsaya dan bata taba ganinta ba anman kamarsu ta baci dan dai kawai khadija ta girme mata khadijan ce tai saurin riko hannunta dan Allah karki fita ki xo muti mgn inkina da kudin bani ba matsala sena tsaya karkiji komai muje sun xauna ta kamo baban nasu ta kawo inda suke xaune yana ganin khadijar yadan wattsake fiddausi ta mike bari nakira wancan banxan yayanta kenan tana tsaki da fada fada ya fito kasan dai kai baka da matsayin da xanje inkiraka dan bukata ta taxo ta xauna kadija tamasa ya kara ji da jiki sannan ta masa bayanin kanta sai kuka haba ni jiki na yabani wallahi tinda naganki furtawa ce nakasa. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Kuka kawai yake dakyar yai shiru nayi danasanin bin shawarar hamxa na cuci kaina tundaga abinda naima saliha nai sallama da farin ciki gashi har yanxu a dana sani nake banjin kuma xan dena haba baba kayi hakuri kadija kitai maka kice kin yafe min koda naji sassauci a rayuwata nine sanadiyar kawo ki duniya ta hanyar banxa nasa mamarki kuka nasani kema kinyi watakilma kina kanyi koda ita vaxata yafenba ke kice kin yafe ko xanji sauki dan Allah baba na dade da yafe ma ban taba rikeka ko tunanin ka cuceni ba na rika na yadda kaddara tace ahaka da gaske kin yafe min nadade da yafe fatana ummata ma ta yafe maka kayya khadija bantaba tunanin akwai randa saliha xata yafen ba. Wadannan sune yaya ba fiddausi da ismail kannenki ne su kadai na haifa sin xame min har nake tunanin gwara ace bani da da dadaisu wallahi haba baba addu'a xaka dinga masa basshi duk tsiya baka isa ka koremu ba dan bamu mukace ka haifomuba inji ismail kinga kiban kudin da kikace xakiban dan kin hanani fita nemowa yunwa nakeji kadija ta bude jaka ta kirgo dubu goma ta vata ta baima ismail ma aiko ta daka tsalle ta rungumeta thanks sis ta fice ismail ya bi bayanta dakinyi shawara dani da baki basu ba. Nayi dana sani mara misaltuwa tun lokacin da nasamu labarin haihuwar saliha naje nadinga xuga babanta dan sanin yadda sukai da bavana babu ta yaddaxa'ai ya yadda nace kedin yatace burina be cika ba na mutuwarki sedai naji dadin korar saliha da babanta yai sedai mai abinda nake tunani xata rasa matsuguni har muje mu kwaceki kamar yadda hamxa ya tsara be yuwuba. Batafi watanni da aureba na auri iklima auren da be karar dani komai ba sai dana sani tun da na aurota nake danasi har yau bandena ba . Watanmu tara da aure ta fara laulayi shekara na xagayowa ta haifi danta yaci sunan babana ismail rashin ta idonta tasa mahaifina yakwace ismail ita kuma yace nasaketa haka kuwa akai duda na saketa bamu rabuba mahaifina da kansa yaban yan kanwarsa ita ta haifi fiddausi gurin haihu ta rasu dan haka yarta ta karba tashayar nakasa rabuwa da iklima kaxalika na kada aure duk yadda namaifina yai yayi nanaki aure duda besan ina tare da iklima ba. Bansan wanda yaje yasanar masa ba be yarda ba dan haka kuwa ya xo dan tabvatarwa ya yarda aikuwa yana komawa gida akace ya fadi iklima ta hanani xuwa xuwa duda kuwa burina be huce naje na ganshi ya yafe minba. Ita tasanya na karbo yarana muka sake aure mafarar lalacewr tar biyarsu kenan domin kuwa ita kanta bata da tarbiyar balle tabaima wasu. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Bawata sana'a nake ba da mahaifina na dogara shima jiki yaki sauki xara bata barin dami komai na kare takai ansayar da komai nasa dan masa magani babu sauki iklima tace babu yadda xa'ai nasaida gidan da muke ciki baxai yiwuba yayata ce tadauki babana wanda matsayinta na mace ba ita yadace ta daukeshi ba duda kuwa banbancin da yake mana kansu matane komai yasamu nine sai gashi sudin sune suka xama gatansa. Kwata kwata iklima ta daina ganin girmana bama tajin maganata in nai magana tace ai ni ne matar itace mijin abokaina duk sun gujeni yarana sun rainani babu wanda na isa nace yayi yayi. Bankara danasanin abinda nai abaya ba sai randa na kama iklima da kato adakina nai kuka nai danasani tun daga wannan ranar cuta taki barina nai magana taci mutuncina tabar gidan. Ahankula duk wani abin anfani na gidannan su fiddausi sun debe sun saida gidanma sai sun gadama nake ganinsu balle insaka ran xasu kula dani dan yayata muhd ne kawai yake xuwa yakula dani duda iyayensa basu sani ba nasan duk sanda suka sani ranar xan dena ganinsa yaron yanasaona katsam iyayensa suka daukeshi suka kaishi waje karatu naci wuya sosai dan banda mai kuladai baufi wata biyu dawowa ba da akwanaki ne baxaki iya shigowaba domin xuwansa yagyaggyara ni. Yanxuma dan dare yayi ne daxaki ganshi yaxo bankara firgita da hakkin wani ba sai yadda naga hamxa ya koma wanda har gara ni sau dubu daganin irin mutuwar dayai ta wulakacin alokacin na tabvatar lallai hakkin wani ba abin wasa bane ko ya yafe ma balle bai yafeba. Baba tare nake da mijina shine bakice yashigo ba tai dan murmushi ai yace xe shigo inyaxo daukata to shikena ta mike dakyar tace ina kitchen yake yanuno mata baxai shigaba yadda yake tsami har wani wari wari yake alamar andade ba'a shigesa ba anbar abubuwa sun rube ciki. Wayarta tasa ta kira jafar inbakai nisa ba dan Allah kaxo ai ina kofar gidan au kace xaka kadawo fasawa nai tai dariya to shigo shi ya tai maka suka sanya shi mota fa'ams special hospital suka kaishi kasantuwar su masana ga kowa basu sha wata wuyaba aka bashi gado satinsa biyu yawar ware har yana tafiya yana iya cin abinci. Khadija ce taxaunar da fiddausi da ismail tai tamusu nasiha da kwatanta musu abu buwa na rayuwa hartasamu suka dan fiskance ta tadauki fiddausi takaima maman jafar dan tasan ummanta baxa karbeta ba tamata bayanin komai taji dadi ta jin jina kadijar shi kuma ismail shi yake jinyar abban nasu intaxo shi kuma ya rafi gida dan yin wanktaba. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Yau khadija ce agurin abban nata burinta yamata bayanin inda yanxu kakansa da sauran danginsa suke dan tanasan ta shiryasu tanasan kakan nata ya yafema abvan nata anman yaki saurararta inta takura masa da maganar saima kuka ko ya rufe idonsa kamar me bacci yanxunma hakance ta kasance ya rufe idon kamar mai bacci baisan taci gaba da maganar da take ms. Ismail ne yashigo sai wani dake biye dashi bata kula da kowane ba dan kanta asa yake sai ji tai ance khadija ko ba ita vace kamar tasan muryar tai saurin dagowa Abba daman kana duniya yaushe ka dawo ta hada masa tambayar lokaci guda yai dariya kafin ya xauna me yakawoki nan bacin nasan ance ba nursing kikai ba bata bashi amsaba kafin tace kai mai yakawoka opppp duk kun kasa bama juna amsa bara duk na baku inji ismail yana dariya yah kadija kenan yah abba kenan yah kadija yayarmuce taxo jinyar abbanmu kamar yadda yake abbanta kaji amsarka bece komaiba yace yah abba dan gidan auty sadiya ne yayar abbanmu uwa daya uba daya babarsa da abba suke. Seda khadija tama abba bayani sosai yafiskanta haba ashe mudin jini daya ne shiyasa nake jinki araina narasa mai yasa tai dariya nima haka kasan mai xakamun sekin fada so nake kasharen hanya naje na nemawa abba gafara sai alokacin ya bude ido muhd yaushe kaxo najejje gida bakanan sai yau na tadda ismail yace kn asibiti yai murmushi muhd dan Allah karka kaita kaji ko bansan abbana yakara kullata to Abba baxan kai taba. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Duk inda khadija xatai da taimakon Allah da tai makon Abba suka samu suka saita abbanta da iyayensa kullum yaxauna shikadai bashi da aiki sai sharar kwalla dan yaga ishara kala kala wai yau ace diyar dayai cikinta dan daukan fansa dan wulakanta uwatta yaso kashe itace ta dauki nauyin komai nasa ta dawo masa darin cikinsa dayake xaton yarasashi rashi na har abada burinsa aduniya yaje ya roki saliha gafara koda baxa yafe masaba. Tsananin ciwon datakeji yasata kasa daurewa duk kuwa da yadda taso daurewa dole ta tashi jafar agigice ya dauketa saiva sibiti tunda aka shiga da ita labour room yake kai kawo bashi ya xauna ba saida Rahma ta fito dauke da baby oga seka ban tukuci kafin ka karbi baby baisan ko nawa ya bata ba ta mika masa Allah ya raya mana shi tasamu namiji yaron na kirjinsa yana faman kiran waya kafin kace mene dangi sun cika asibitin dakyar ya iya basu yaron danma tsoffi sunfara masa tsiya. Khadija kam taga gata taji dadi dangi ta ko ina xuwa ake ta bangaren ummanta abbanta babanta yan uwan jafar kawaye da abokan arxiki kowa burinsa yaxo yaga dan dja. Yau ummam khadija tafi kowa farin ciki wai yau itace dauke da dan khadija ahannunta danta data haifa ta hanyar aure abinda aka sha mata gori akai itakam ko yau ta mutu ta godema Allah ya cika mata burinta aranar aka sallamesu agidanta xasuyi sunan kasantuwar da dama basu san gidanba daga baya se taje wanka gidan mama. Jafar ne rike da babyn wai wane suna kikeso asamaine duk wanda kaxaba masa kaida tun yana ciki kake nuna iko dashi yai dariya am serious na baki xabi tukuicinkine shike indai nice kasa masa muhd nasir kamar kin shiga raina wallahi sunan naketa Addu'a Allaj yasa kixa ba tai dariya. Ranar suna yaro yaci sunansa Nasir suke kiransa da sagiree yadda khadija taga yan uwa ta ko ina yafi komai mata dadi dan burinta ya cika ta ko ina sai daya datake san ummanta ta yafema abvanta. Dakansa yaje har gidan yai sa'a mahrax yana gida ya ganeshi yai mai iso har ciki aiko tana ganininsa ta hau fada me yakawoshi gidanta kuka wiwi yadinga mata yana magiya har saida yabata tausayi abinka da xuciyar mata mai sanyi tuni ta yafe masa. Khadija tafi kowa farin cikin samin lbrin ummanta tace ta yafema abbanta. Ita da kanta ta gyara masa gidansa tanaimo masa mata ta bude masa shago anan wanbai ta bashi halak malak. Yaukam da alhini suka tashi domin kakanta ne Allah yai masa rasuwa na gurin uba tai kuka ba na wasa ba domin yan kwanakinnan sun saba sosai mutunne mai iya xama da jama'a ta ko ina. Wani abu da yakara baima abban khadija tsoro da saka masa tsoron ubangiji shine yadda bayan wata daya da rasuwar mahaifinsa yana xaune a shago wata almajira taxo bara bema ganeta ba saiji yai tace muktar yadan kalleta vanfa ganeki ba iklima ce matarka babu tayadda xa'ai kace itadince iklima yar kwalliya mai kyau daji da gayu itace ta koma haka babu hannu daya duk tai baki wasu kuraje duk sun fito mata a fuska yabata sadaka yanaji tana magana baice da ita kalaba tabar gurin. Yaukam hargida taxo tana kuka ta naimi gafararsa dasaka bakin ismail ta ya yafe mata tace ina fiddausi ismail ya kirata taji dadin yadda diyarta ta kintsu gida mai matsakaicin girma aka kama mata suka kaita asibi. Ashe bayan barinta gidan gurin saurayin nata ta koma suka ci gaba da iskancinsu ashe yanada kanjamau sunje asibiti bata da lpy anan suka gano itama ta kamu aiko tun ahanya suke xabga bala'i kan ya cuceta bai kulaba sukai karo da wata tifa nan take baiko shuraba itama saida tai jinya mai yawa aka yanke hannunta da yarube lokacin data fito daga asibiti babu inda xata dole ta kama bara. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Abu kamar wasa sai gashi yaxama gaske dan tun ran sunan sagiree Abba da muklisa suka fara soyayya duda cewar ta koma sakkoto dake tana xuwa hutu har gidan khadija take xuwa yanxu andena mata rashin kunya dan ta girma tagano ramine kawai kishir mamarta take jefata dan rabakanta da yan uwanta. Magana kam tai nisa dan gar manya sun shiga ciki watanni ya rage asha bikin nuklisa da Abba ismail da bintoo me aikin umman khadija da tuni taxama ya dan umman tai mata komi fiddausi da muktar cousin din su jafar. Khadija kam tayi uwa yadda ta xage da aljihunta da karfinta abikinnan ita tai kayan dakinsu komai akace ana bukata bakyashi ko wani tunani xata bada kowa kagani ita yabonta kawai yake. Duda kasan tuwarta da tsohon ciki bai hanata xagewa wajen fidda kannen nata kunya va tako ina sudai iyayenta da yan uwanta sai san barka. Haka nake sanki Na F.A.Ya'u Khadija taxama matarsa abarso ga kowa kowa kagani kai har wanda basu wani hada alakaba burinsa a budi baki ace KHADIJA SALIHA YAKASAi yar uwarsa ce. Kowa cikin dangi yaro da babva inya kwaso matsalarsa kai tsaye gurinta yake xuwa dan sanin vabu kyashi ko wulakanci xatai masa. Yanxu khadija an na daya daga cikin manyan pharmacist din da ake ji dasu a nageria dan lokacin da jafar yaje waje danyin wani course ya tafi dasu ita da yaranta acan tai PhD dinta kasantuwar tun bayan haihuwar shukra ta kammala masters dinta a zariya kaxalika pharmacy dinta ba wai arewa kawaiba kusan yawanci garuwa ta bude branch dinda yayin da kasama ke alfari da ita bawai iyalinta bama. Itakam khadija saidai ta godema Allah akalla akarjashinta batasan iyakar wadanda kecin abinci ba kama daga masu PhD,masters,degree bama amaganar masu diploma ko NCE fannin health burinta ace yau tabada gudunmawa a drug discovery tasani balallai ta iyaba hakan yasanya ta dage wajen taimakawa na kasa masu tasowa wanda ko bayan ranta xataso ace yau ga dan nageria shine yagano wani maganin da duk duniya tayadda dashi take kuma amfanarsa burinta ace ta bangarenta wannan wanda ko waccen xasu gano din. Wata shawara na kawo mana inajinka maixai hana kixama dealer ta magani kiyi register ki bude kamfani kana ganin xan iya xaki iya matsalar ma'aikata babu matsala kinsani kema bata dauki abin da mahin mancin ba ta basar da batun. Yau suna xaune yakuma xuwa da batun har ya gama komai sunan kanfanin kawai yakeso tasa tai shiru can tace SALIHA pharmaceutical therapy ngl. bai musuba ya sanya basufi wata uku da batunba kanfani ya fara aiki ma'aikata kam harsaida sukai yawa. Masallatai da fanfuna data gina basa misaltuwa banda makarantun islamiyya waau ta sadaukar ga nasir wasu ummanta wasu kanta wasu family dinsu kai har makarantun gwammnati intaga na bukatar gyara haka take xuwa tayi gabaki daya tanayi ne batare da nuna ita din take ba. Zaune take tana baima Nawas mama shukra na game yayin da sagiree ke muraja'ar haddarsa mami na na kallo ummi tashigo da gudu ga abba ga abba mts shukra tai tsaki mu dallah malama kimana shiru sekace abban unguwa yaje ina bacci ma yake to bagani nai bai tashi da wuriba momy tunamin nan inji sagiree takarva tana biya masa maman yara ana hirar ne tai dari dadyn yara sarkin bacci har ka tashi natashi xan tafi gurin kanwariki tai dariya to agaishe ace wai ita yaushe xata yadda a aurota ne inganta yai waje yana dariya kayi mantuwa baka dauki gift dinba kingani ko duk na sha'afa santa ya rufen ido yafi minti biyar a tsaye abakin kofa yana kallonta ta gama biyana sagiree mami ta miko mata biro momy rubutamin love wallahi seta fara rubutan agogo inji ummi kinga ummi bansan rigima ta rigaki kibari infara mata ya shigo au har kadawo yai dariya waike dan Allah yaushe xaki fara kishi tai murmushi se randa kadena wannan wasan au kinma gane wasane ko nasan mexanyi sena gano wane irin kishi ne dake hmmm tunda kace haka baxaka ganoba haka kikace eh mana tan shikenan xakisha mamaki ya xauna ya kamo hannun ummi kawo inxana miki agogon ta mika masa yayinda mamin tace bata yadda ba itama dady ne xai mata kaga yaran dady da momy ya rungumosu sagiree da shukra suka maxo muma ahada damu to ai sai a hada da momynko ya hada gaba daya ya rungume kayansa dadi ya ishi kadija yau itace cikin iyayinta gata ga mijinta ga yayanta gashi taxama abae so ga kowa basauran gori Ahankuka ta furta alhamdulillah. Nima anan nakesan cewa Alhamdulillah ina mai godema Allah da yakawoni karshen wannan littafi fatana a'anfana da abinda aka karanta na rubutane bawai dan cin mutinci ko cin xarafin kowaba sai dan nishadantarwa fadakarwa da ilmantarwa bakuma ya nufin koyi ga rayuwar wani ko waba na kirkira ne kawai. Wani abu danake san fuskanta game da labarin duk yadda ka tsinci kanka akwai mafita inkai hakuri dayardar Allah xaka ga sauyi da farin cikin da baka xata ba. Zamantowa maihakuri da yafiya da maida komai bakomai bane wani babban matakine na rayu cikin farin ciki da cigaba duk girman lefin da mutun yama xaka iya yafe masa domin kai bakasan mexaka ma wani a gaba ba. Duk yanayin da ka tsinci kanka wani yafika walau na farin ciki ko akasinsa kasanto mai godema Allah akoyaushe. Zamantowar mutun mara uba bashi yake nufin shidin ba mutumin kirki bane bashi ke nufi baxa'a hada auratayya dashi ba. Karka taba xama mai korafi dan iyayenka sun haifeka suna talakawa sunma gata sun haifeka da aure. Karka taba korafin iyayenka sun cuceka sun haifeka ba aure kagodema Allah dayaika musulmi hakan baya nufin karshen farin cikinka arayuw dayawa ana kuskure wai dan anhaifeka ba aure sai kace baxaka xama na gariba ai anriga an bata ma rayuwa hakan ba dai dai bane ko kaga uwa ta rike dan inya girma yace bashi da abin ki sai ita bacun ita kanta ba'asan ranta ta haifeka ahakaba takuma jure bata yadda kaiba harka girma kasanta wani yanacan bemasan kowa nasa ba burinsa kuma yaga koda uwattasa ce koda itadin kuturwa ce mahaukaci makauniya duk xai dauka indai xa'ace yau ga mahaifiyarsa. Duk wani kuskure dake ciki ina fatan amin afuwa dan adam ajixine GODIYA. Godiya gami da jinjina gaduk wani ko wata da suka karanta wannan littafi nagode Allah yabar xumunci. Taku dabance. Usaina muhd ibrahim Aisha muhd ibrahim Zainab shehu umar Nafisa shu'aib Fatima Hasan Abbakar Semun sake haduwa awani littafin mai suna yar'amana. 09028287218 adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *