Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, April 3, 2017

hakan take

adsense here HAKAN TAKE part 1 HAKAN TAKE part 1 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 16:11 Wata shimfidaddiyar ni'imace tasauka tamamaye dukkan sassan gari baki daya Bayan dauke ruwa adaidai lokacin da mangariba yana daaba karatowa.. Ahankali take tafiya kanta na kallon sama tamkar tana duban wata.. Hannunta rike yake da makullin motarta yayinda take wasa da 'yan key din ahannayenta. Farace doguwa mai matsakaicin jiki daidai misali fuskarta madaidaici yake tamkar yadda takeso aka zana matashi aduk lokacinda tayi murmushi zakaga dimple dinta sundanyi motsi tareda lotsewa kadan zuwa ciki hanci tsiriri maidan madaidaicin tsayi kallo daya zakayi mata natabbata sai tayi awon gaba da duk wani nitsuwa dake tattare da zuciyarka komin ya kamewarka take duka duka bazata wuce 'yar kimanin shekaru 17 ba.. Me yake mata dadine awannan duniyar babu alamar kunci ko 6acin rai atattare da ita yayinda take tafiya cikin walwala . Awani 6angaren kuma idan kakare mata zuciyarka takan iya saka maka cewa lalle wannan lafiya ne ya isheta bayaga lafiyarma akwai wani alheri data samu. Basai ansanar dakai ba kasan wannan tafito ne daga babban gida ma'ana gidan manyan mutane idan zakayi saurin yanke hukunci kana iya cewa wannan dangi ce kokuma zuri'a data samo asali daga gidan sarakai kokuma wasu hamshakan attajirai wadanda sukan iya shiga ko ina a duniya sunemo aure kuma abasu koda kuwa akasar saudiyace. Bayan kare mata kallo da Sagir yayi yayinda yazauna ya na fakonta adaidai karkashin wani itaciya wanda idan mutum yana zaune ba lalle bane kagane cewa akwai mutum awajen. Har zuwa lokacin da ta karisa zuwa cikin motarta tashiga, Tashinta keda wuya Sagir yaciro wayarsa yakara abisa kunnensa nahagu tareda cewa Hello Rilwan kuyi kokari kutareta yanzu haka tatashi kada ku bari yau muyi missing din wannan target din.. Ok kawai Rilwan yafada tareda cewa karka damu sai kayi kokari kaima kabiyota abaya, As how banida ko keke zakace nabi wanda yake tafiya da mota kaga na tabbata wannan hanyar zatabi idan kuma kukasake ta kubce mana wallahi yau zakusan yadda zakuyi damu. Ok bamatsala Rilwan yafada sanna yajuya tareda kallon abokinsa Awwal bross yarinyannan fa ta taso daga yanzu haka nasan hanyar gida take sabida haka katashi muje Muyi abinda yadace Ok dasauri awwal yatashi suka doshi kan hanyar datake bi kafin taiso gidansu. Tafiya take cikin annashuwa yayinda tasaka wakar akasi Na nura m inuwa tanaji tana gyada kai sannan kuma tana bibiyar abinda ake fadi acikin wakar. Kwatsam sai tacikaro da mutum akwace agefen titi tamkar wanda aka bugeshi damota sannan aka ki tsayawa adaukeshi sai faman juye juye yakeyi kamar wanda ake famar zarewa rai. Dasauri ta katse wakar yayinda ta taka birkin tareda fitowa tana salati Innalillahi wa'inna ilahi raaji'un jama'a kuzo kutaimakeni tajuya gabar yamma kudu da arewa babu alamar wani mahaluki awajen tasauko har inda yake ta durkusa alokacin tausayinsa yakamata yayinda idanunta suka fara cikowa da kwalla cikin juriya ta karesu tareda komawa tabude motar ta danufin koda janshi zatayi zuwa cikin motar sabida tasami ceton rayuwarsa adaidai lokacin saiga Wani saurayi ya iso ahankali yana tafiya dasauri ta tashi ta taresa malam dan Allah kazo kayi taimako wancan mutumin ne baida lafiya bansan me yasameshiba anan naganshi nima. Tana magana hankalinta atashe tamkar ubanta ne awajen baice mata uffan ba kawai yanufi wajen dagudu yaje wajen tareda ambaton sunan wanda yake kwancen Awwal meyasameka? Bai tsaya jiran amsa ba kawai ya daukesa kamar jariri yanufi cikin motar budurwar yasaukeshi sannan yace dan unguwarmune kitaimaka kigaimu gidansu. Tace ba matsala. Tashiga taja motar tana cikin tafiya yayinda yake yima wanda yake kwancen fifita yajefa mata tambaya. 'yan mata ya Sunanki? khairat , Kawai tafurta batareda tace wani abuba. Malama khairat gaskiya kinyi kokari Allah yasaka da Alheri . Ameeen amsar data bashi kenan. Shiru suka danyi na 'yan dakikai sannan tajefamai tambaya kaifa ya sunanka. Rilwan sunana kenan. Dakyau Rilwan har yanzu bamu iso unguwar taku ba? Yace eh saura kadan.. Ba'a jimaba suka fara fita bayan gari can sai yanuna mata wani gida wanda bisa dukkan alamu ko gama gyaran gidan ba'ayiba yace mata canne gidansu. Ba musu ta kada kan motar har zuwa kofar gidan, gidane Babba wanda ake kan gyaransa yayinda angama gini da komai saidai ba'ayi plasta din gidan ba balle fenti, azuciyara take saka anya kuwa akwai mutane awannan gidan? Duk da haka bata tsaya ba sabida alokacin magriba ya tsananta karatowa. Ahankali Rilwan yafita yabude mata gate din gidan tashiga sannan yarufe bayan tashigo tasami waje tafaka . Sannan tafito har yanzu hankalinta atashe yake. Takallesa tareda cewa yanaga gidan babu alaman mutane? Kawai murmushi yasaka tareda cewa malama khairat we are sorry for betraying you awannan gidan babu mutane kawai munyi kidnapping dinki ne wanda kike zaton baida lafiya lafiyansa kalau. Da sauri tajuya arikice yayinda idanunta suka sauya kala daga farare zuwa pink tadubi cikin motar yayinda takalli awwal yataso ahankali yana dariya. Hhhhhhh bross mission is now completed yafada. Tayi yunkurin zatayi ihu Rilwan yace mata bamatsala zaki iyayin duk ihun dazakiyi anan babu wanda zaizo yataimakeki. Idan bakisani bama gara kisani nan gidan sunansa ihunka banza. Duk irin ihun dazakiyi abanza zakiyi shi, Yana cikin bayani yayinda awwal yakunna kida amotar tareda kure volume yana gyada kai, Ji kawai sukayi ta yimwuf tanufi bakin kofa kama kofar keda wuta ta finciki kofar take yabude bude sai dai kash tayi Rashin Sa'a adai dai lokacin Sagir yadawo yana dabda bude kofar hankadota ciki yayi sai da tafadi, Kai me haka Ril HAKAN TAKE part 2 HAKAN TAKE part 2 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 16:39 yakarisa zancensa dacewa matukar kuka saka 'yan sanda acikin wannan case din duk abinda yafaru da 'yar ku kuka jawo. Toh Hajiya ta amsa sannan takara dacewa dan Allah karkayiwa 'yata komai duk abinda kakeso za'a baka, yace ok toh ina bukatar zantawa da Alhaji cikin gaggawa. Hajiya takatse kiran sannan ta kira lambar Alhaji Haruna, alokacin yana cikin masallaci hakan yasa yakatse kiran tasake kira yakuma katsewa ,tasake kuma kiransa nanfa jikinsa yabashi cewa lallai duk yadda akayi yau ba lafiya ba. Kashe wayar Gabadaya yayi bayan ya idar da Sallah yagama addu'arsa kafinnan yafito daga masallaci yakunna wayarsa sannan yakira Hajiya, dagawarta keda wuya yaji muryarta a dishe bisa dukkan alamu kuka yaci karfin muryar haba Alhaji ai yakamata kagane daga ganin Irin kiran danake yimaka ai ba lafiya ba, Cikin 'yan kankanin lokacin hankalinsa yatashi Hajiya meke faruwa ne dan Allah yajefa mata tambaya wasu mutane ne suka sace Khairat tunda ta fita da rana kitso wajen kawarta har yanzu bata dawoba nakira wayarta ma wani ne yadauka wai sai anbashi kudi zai saketa ok . Toh gani nan zuwa ina kusa dama , Alhaji Hankalinsa atashe yadubi driver dinsa yace mutafi gida yanzu yanzunnan, ranka dade lafiya kuwa naga daga magana awaya gabadaya hankalinka yatashi. alhaji yace wai wasu ne sukayi kidnaped din 'yata Khairat, subhanallahi yaushe kenan yafada yayinda shima tashin hanlali yaziyarceshi,yanzu sanr dani akayi kenan Alhaji yabashi amsa, Allah yasa aganeta cikin koshin lafiya, Alhaji yace ameen, acikin palo yasameta tahada kai da guiwa tana kuka haba Hajiya kikwantar da hankalinki insha Allahu zata dawo cikin koshin lafiya barima insanarwa jami'an tsaro Alhaji yaciro wayarsa zaiyi kira Hajiya tarike hannunsa tareda fadin sun gargadeni akan shigarda jami'an tsaro cikin lamarin namanta ne bansanar dakai ba sukace duk abinda yasameta mu mukaja dan Allah Alhaji kayi hakuri 'yata tadawo cikin koshin lafiya. Alhaji jikinsa amace yatsaya yadanyi shiru sannan yace bari nakirasu muzanta dasu, yakira wayar khairat alokacin suna zaune Sagir yana bata bayani 'yan mata kin bamu wahala munjima muna fakonki sai yau Allah yabamu ikon kamaki, ita dai mamaki take tagama karemusu kallo baki dayansu babu wanda zai kai koda shekaru 20 dukda cewa bata san shekarunsu ba amma idan zata kamanta a idanunta bazasu wuce 'yan shekaru 18 ba. Rurin wayarta ne yakatse ta daga sakarzuci datakeyi. Yawwa ga kiran Alhaji Sagir yafada yayinda yajuya tareda kashe ma 'yan uwansa idanu (signal) mikomin wayar Rilwan yafada yayinda yakuma matsowa kusada khairat, yaa Alhaj yafada yana dariya, Alhaji bakinsa na rawa yace kaga malam basai kafadamin ba nasan kaika dauke 'yata amma dan Allah kataimaka kafadi nawa kakeso sai mubaka kasake mana 'yar mu , yawwa Alhaji yanzu kayi zance bari nakuma tabbatar maka cewa 'yarka tana hannunmu Rilwan yariko gyalenta tareda fincikota, tasaka ihu wayyo Allah Abba kataimakeni zasu jimin ciwo, Alhaji yakara dimaucewa kaga dan Allah kasaurareni ko dar Rilwan baiyiba yakuma ce ina fatan matarka ta gargadeka kan shigar da 'yan sanda cikin wannan case din? Alhaji ya amsa dacewa Eh, nawa kakeso nanfa Rilwan yadanyi shiru sai yanzu yatuna basuyi shawarar nawa zasu yanka a basu ba, Yace bari nayi shawara da 'yan uwana kakirani bayan 1 minute yakatse kiran sannan yadubesu yana murmushi ya guys nawa kukega zance abamu awwal yace kuut kace masa dubu hamsin Sagir yace haba dubu Hamsin yayi kadan kace musu dai dubu saba'in. Ji sukayi kawai ta tuntsire da dariya dasauri suka waiga ke dariyan me kikeyi sagir yajefa mata tambaya. Ah babu ta amsa , yayinda take kokarin toshe bakinta bisa dukkan alamu kubce mata dariyar yayi. Awwal yakariso inda take yayinda yamatso dab da ita ke karkiyi kuskuren raina mana Hankali fa? Dariyan me kike? ko dar batayi ba tace amma ku baku ta6a yin kidnapping bako? Uhm meyasa kikayi mana wanna tambayar karka damu zan baku amsa, amma abinda nakeso daku kawai kuce abaku dubu dari 2 inaga zaku dade kuna kancal dashi ko? Sagir yajuya yakalli Rilwan yayinda yadanyi shiru sannan yasaukar da murya tareda fadin kungani shine nake gayamuku ku garori ne gashi kunsa har tagano lagonmu, yanzu kawai muyi kokari mu sanar masa yanda za'a bamu. Awwal yace to muce dubu dari biyun kawai. Suna cikin zancen saiga kiran Alhaji yashigo Rilwan yadauka yace Alhaji dubu dari biyu kawai zaka bamu musake maka 'yar ka, Alhaji yace toh toh toh yanzu a'ina za'a baku kudin kufadi inda kukeso nida kaina zan kawomuku kudin sai ku sakemin 'yata, dirkashi Rilwan yakara jan numfashi sannan yakumace bani 1 minutes zan fada maka wajen. Nanfa yakatse kiran Alhaji, abin yabawa Alhaji haruna mamaki wadannan kuma wadanne irin 6arayi ne ko shawara ma basuyi mai kyauba, hajiya tadubesa ikon Allah zamani wai yaran attajirai basu isa su sake yanda suke so ba? Wai akan dubu dari biyu suka rikemin 'ya? Hajiya tadubesa o zamani yanzu haka irin yaran nanne marasa aikinyi, a6angaren su Rilwan kuma bayan ya katse kiran sai yatambayesu a'ina kukega zamu ce akawo mana kudin? Shiru suka danyi sannan sukayi zance kasa kasa yanda khairat bata jiba balle tasake tsoma bakinta ciki. Ana haka saiga kiran Alhaji Haruna yaske shigowa. Rilwan yadaga yace Alhaji munaso ka kawo mana kudin kai kadai dakanka bamu yadda kazo koda da driver ba, abayan stadium akwai wata bishiyar gamji kawai ka ajiye kudin awajen sai kayi tafiyarka kawai kakoma gida batareda 6ata lokaci ba zakaga 'yarka tadawo idan kayi kuskuren hakan kuma sunan 'yarka sorry Alhaji yace toh shikenan . Yasanarwa hajiya yadda sukayi cikin hanzari yadauko kudin yakulle abakar leda yasaka acikin aljihun garensa sannan yafita tareda kiran driver dinsa yakar6i makullin motar dake Hannunsa yace bari naje nazo driver yace toh Alhaji bari nakaika mana. Alhaji yace a'a zanje batun yarinyar nan ne kagane yanzu zan dawo , toh Allah yabayyanta cikin lafiya ya amsa,Alhaji yakama hanya, Rilwan yace Awwal kai zakaje kadauko mana kudinnan kaikuma Sagir zakaje kakula da duk shige da ficen da Alhaji Haruna zaiyi idan kaga alamun jami'an tsaro sai kayi gaggawan sanarda Awwal kar yaje yafada tarko inaso wayoyinku yazama mai amfani ayanzu toh suka amsa nikuma zan zauna tareda ita duk abinda ake ciki zamuyi conference call, Alhaji Haruna baitsaya ko inaba sai bayan stadium yaduba gefen hagu yakalli itaciyar gamji da kidnappers din suka fada masa. Sannan ya ajiye kudin awajen jikawai yayi wayarsa tana ringing yadauka sai yaji ance yawwa nan wajen yayi kawai kashiga motarka katafi ya amsa da toh, yajuya yashiga motarsa tafiyarsa keda wuya awwal yazo yadauki kudin cikin hanzari yakama gudu har zuwa inda yatabbatar babu wanda zai yake biye dashi sannan yafara tafiya ahankali, Alhaji Haruna yakirasu yace na kaimuku kudin yanzu sukace eh mundauka yanzu haka amma sai mun kidaya su tukunna idan basu cika ba koda da naira 1 ne 'yarka bazata dawo ba. Alhaji yace Natabbata suncika ma, suna cikin zancen saiga Awwal yashigo yana haki dakudin ahannunsa, ihu kawai suka saka tareda shewa kudi yasamu suka kidaya kudin dubu dari biyu cib sannan suka fara zancen yadda zasu saketa , Rilwan yadubeta Malama khairat sai hakuri fa muna Godiya dakika bamu hadin kai muka samu kudadennan sabida haka zaki tafi da motarki ke da kanki, ta danyi murmushi nagode amma inaso kubani amsoshin wasu tambayoyi wadanda natarasu araina yanzu. Toh muna sauraronki? Amma ku baku ta6a yin kidnapping ba ko? Kuma baku saba yin sata bako? Dakata Awwal yakatseta tareda cewa me kika gani har kike sakar cewa bamu ta6a yin kidnapping ba? Tadanyi ajiyar zuci sannan tace nakalli abubuwa dayawa, dafarko banga bindiga ko wani makami ahannunku ba wanda nasan duk wani 6arawo yana amfani dasu, ke mukike kira 6arayi sagir yanufo kanta kamar zai mareta daga masa hannu Rilwan yayi alamun yadakata nanfa yatsaya,Rilwan yace cigaba dazancenki. Sannan kuma kidnappers suna rufewa mutum idanu sukaisa duk inda sukeso idan sunkaishi nanma cikin kurman daki zasu ajiya mutum ahakanma sai sun dauresa amma ku kuma kun sake har sallah nayi, Nasan kuna mamakin yadda nace kuce abaku dubu dari biyu ko? Toh wannan ba abin mamaki bane naga alamun cewa zakuyi asara ne ace yadda kuka ajiyeni anan natabbata kunada matsalar kudi sosai da ace naga damar kamaku da yanzu haka idan nakoma gida agobe ko wannenku zai dandana kudarsa amma zan rufa muku asiri sabida baku ketamin mutunci na ba, sannan kuma ina mai shawartarku dan Allah ayi kokari anemi sana'a , awwal ya fusata haba Rilwan kanaji irin bakaken maganganun da yarinyarnan ke furtamana, daga dan yatsarsa yayi tareda daurawa akan le6ensa alamun awwal yayi shiru. Shi Rilwan kallonta kawai yakeyi tana zance yanaji amma shi hankalinsa ba'a zancen nata yakeba ya kallon kyawun fuskarta dukdacewa darene amma kasancewar ana farin wata yasa kana iya ganin komai, khairat ta tashi tareda cewa nagode da kuka bani damar furta duk wata zantuka nayi muku tambaya baku amsa ba. Natabbata kunada amsoshin tambayar amma zan adana wannan tambayar acikin zuciyata duk ranar da na hadu da daya daga cikinku sai na tilasta masa amsa wannan tambayar. Tsayawa kawai sukayi suna kallonta har taje tashiga cikin motarta sannan ta tayar tareda lekowa takalli Rilwan kaine ka budemin kofa dazan shigo yanzu kuma bazaka bude bane kome kake nufi? Kai wallahi wannan yarinyar bazata tafi ba kanajin irin zantukan data keyi Sagir yafada yayinda yaje yabude kofar motar yafito da ita yakama gyalenta yashaketa dashi yana faman jijjigata ransa a6ace zaki raina mana hankali dasauri Rilwan yaje yarikeshi ya 6an6are hannunsa daga jikinta sannan yace masa calm down bross shiga motarki kitafi bata kara cewa uffan ba dan taga tabbacin zata iya shan suburbuda awajen Sagir. Rilwan yaje yabude mata kofa sannan tafita tahau kan hanyar gidavels / HAKAN TAKE part 3 HAKAN TAKE part 3 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 16:41 Tafiya take tana dukan sterin motarta tana ciza baki wani zuciyar yana saka mata cewa yanzu me zata fadawa iyayenta wani tunanin kuma yace mata ai sun san abinda yafaru tana cikin sake sake yayinda tashigo unguwarsu jitayi wayarta yafara ringing tasa hannu tadauka Hello Abba tafada cikin sheshshekar murya ya amsa khairat kece ta amsa eh nice Abba yanzu haka nakusan dawowa gida , cikin farin ciki yace kina daidai ina tace Abba gani nan akusa da gida Alhaji yace toh shikenan yakashe wayar tareda hamdala yadubi hajiya sai godiya yanzu haka tana hanya harma takusan isowa gida, baigama rufe bakinsa ba sukaji horn din motarta alamun tadawo kenan, hajiya cikin farin ciki suka fito tsakar gida yayinda mai gadi yabude kofa yace sannu da dawowa Khairat sannu ta amsa yawwa baba maigadi. Tawuce taje tayi fakin sannan tafito dagudu tana kuka ta rungumi ummarta ita ko sai rarrashinta kamar wata jaririya, mesukayi miki 'yata umma babu abinda sukayi min wlh hajiya tace a'a kidai fada mana gaskiya kinga mu iyayenki ne, Alokacin Alhaji ya'iso wajen nan fa taje dagudu tafadi ajikinsa kamar yadda tayiwa mahaifiyarta Alhaji yasaka hannu yashare hawayen daya cika mata fuska tambayar kenan mesukayi miki tace abba wallahi bakomai, alokacin driver din Alhaji yakariso wajen tareda fadin khairat sannunki dadawowa ta amsa yawwa ina fatan basuyi miki rauni ba? Kai wannan tambayar dai ta isheni haka tafada azuciyarta, Alhaji yadubesa yace eh wai haka tafada amma ni inaga kamar ta6oye mana ne, duk zancen da sukeyi Baba mai gadi yana jinsu shima nan yafito yadubesu tareda fadin haba Alhaji Haruna ai kamata yayi kubata dama tahuta hankalinta idan yadawo sai ku tambayeta cikin nitsuwa eh tabbas wannan zancen hakane , hajiya takama jikin khairat suka shiga cikin parlo sannan ta kawo mata abinci taci kadan, bayan tagama taje tayi wanka sannan sukace taje takwanta tahuta saigobe zasuyi mata duk wani tambayoyi dasuke so, a6angaren su Rilwan kuma daga lokacin da khairat tafita daga gidan basu tsaya ko ina ba sai gidan dasuke da zama wato gidan marayu, dama su agidan ma dakinsu daban ne kasancewarsu sune manya agidan hakan yasa aka ware musu 6angarensu na daban cikin daki suka wuce kai tsaye, agidan akwai yara kanana maza da mata sannan akwai madaidaita, Aisha tana daya daga cikin 'yan mata marayu dake gidan wacce zata kai kimanin shekaru 13 da haifuwa kusan itace Babba aduk 'yan matan dake gidan suna karatu sannan suna islamiya amma yanzu gabadaya gwambati tayi watsi da lamarinsu ba'a damu da kaimusu abinci ba, awani lokaci ma haka suke kwana da yunwa, wahala tazame musu riga sannan yunwa kuma yazame musu jiki, makarantar da wani tsohon dan majalisa yabude na marayu dinma yanzu haka duk malaman makarantar sun watse sabida ba'a biyansu albashi tunda wa'adin mulkinsa yakare, awani lokaci attajirai sukan kawo musu gudunmawar abinci da wasu kayayyaki amma ayanzu haka duk abubuwan Babu, Baaba jummai itace wacce aka dauka domin girka musu abinci Allah yasaka mata da alheri dukdacewa tayi kusan watanni gomasha biyu batareda anbiyata albashinta ba amma hakan baisa tadena dafa musu abinda zasu ci ba, matukar akwai abinda wasu attajirai zasu kawo koda watanni ne bazai hanata girka musu ba, dukkannin masu kula da lafiyar yaran sun watse musamman kanana babu mai yimusu wanka balle wanki sai Baaba jummai awani lokacinma kudin sabulu ko omo ma gagaransu yakeyi , Tun Baaba jummai tana bin wajajen shugabanni tana kai kuka bisa rayuwar marayunnan har tadena babu abinda ya sauya, lokaci daya ne suke samun walwala lokacin yakin neman za6e nanfa zakaga 'yan siyasa daga wancan jam'iyyar zuwa wannan kowa yana kaimusu gudunmawa tareda karyace karyace amma dazarar anyi za6e angama bazaka sake ganinsu ba sai wani lokacin siyasar. Duka duka yanxu yaran dasuka rage agidan basu wuce 15 ba wasu sun rasu wasu kuma 'yan uwansu sun bayyana sun daukesu , Bayan su Rilwan sundawo Rilwan yafito tsakiyar gidan yana kira A'isha ta amsa dasauri tafito gani yaya Rilwan yadubeta yau anyi abinci agidannan kuwa? Tace a'a wlh tundasafe babu abinda akayi yanzu yaran ma duk sunyi bacci, yace baaba jummai fa? Tana can dakinta itama banyi tsammanin taci wani abu yau ba inaga kamar ma bata jindadin jikinta, yace toh shikenan bari naje nanemo mana abinci sabida yau munje munyi sana'a munsamo kudi dayawa tace Allah ko yaya? Yace mata eh kije kizauna bari nasami su Sagir suna daki sai muje, idan muka duba Baaba jummai sai mu wuce sayan abincin tace toh, Rilwan yaje yasanar masu sagir suka fito sukaje dakin Baaba jummai tadubesu yau yarannan ina kuka shiga tunsafe naketa jajenku sai yanzu karfe10 kuka dawo cikin karfin hali tafadi sukace baba munje neman kudi ne tace Alhamdulillahi Allah yasa dai kunsamu, suka amsa eh munsamu tace wane irin sana'a suka danyi shiru sai kalle kallen juna sukeyi sai Awwal yace leburanci mukaje , tace yayi kyau badacan kukace bazaku iya ba, sagir yace baaba ai dolenmu yazamuyi muna marayu ai babu maraya sai rago, tace hakane, Rilwan yace baaba kamar dai bakiji dadi bako? Baaba tace Aisha ce ta gayama haka ko? Yace eh tace hakane kaina kemin ciwo kuma yanzu yadena, sukace Allah yakara sauki yanzu, me zamu sayo baaba jummai tace kudin dayawa kuka samu ne? Rilwan yace eh dayawa muka samu , tace nawa ne? Sai yadanyi shiru yakalli sagir Awwal yace dubu ashirin ne, dasauri tatashi daga kwance datakeyi. Ina fatan dai ba sata kukaje kukayi ba? Ah haba baaba yaza'ayi muyi sata kuma Rilwan yafada , cike da mamaki tace toh? nidai gani nayi kamar bazaku iya aikin dubu goma awuni daya ba, balle dubu ashirin kuma nasani leburanci akwai wahala. Uhm baaba kenan ke ai tsohuwa ce kinga dole zaki ga aikin zaiyi wahala amma mu dayake yara ne ai bazamuga wahalar aikin ba, tace toh yanzu dai sai kuje kunemu abinci buhun shinkafa zaku sayo tareda kayan miya irinsu gishiri,magi, da borkono dasauransu, duka kudin da zaku kashe kar yawuce dubu 15 shabiyar sauran kuma sai kuyi tanadi nangaba zaiyi muku amfani, suka amsa toh, tareda godiya sannan suka fita daga dakin suna tafiya awwal yace gaskiya abinda baaba jummai dinnan take mana koda uwar data haifemu illa iyaka, hakane gaskiya saidai muce mata Allah yasaka mata da alheri. Sukaje suka sayo duk abubuwanda tafada suka kawo alokacin tayi musu girki akabi aka tashi kowanne yaro daga bacci yaci abinci sannan yakwanta, a6angaren khairat kuwa bayan takwanta akan gadonta sai bacci yakasa yin awon gaba da ita kawai tana maimaita zantukan da 'yan kidnapping sukayi mata, (babu wani abinda zamuyi miki kawai hadin kanki muke bukata idan kuma kika butulce mana duk abinda mukayi miki ke kikaja.) (angaya miki mu mutanen banza ne ? Mu kudi kawai muke bukata)(mungode dakika bamu hadin kai harmuka sami abinda mukeso Allah yasaka da alheri) maganganunsu kenan dayake ta kaiwa da kawowa acikin kwanyarta, tabbas bisa dukkan alamu wanda suke kira Rilwan dinnan shine shugabansu dan naga da shawararsa suke amfani amma wadannan fa basu da wayo zan iya komawa gidan kuma zan samesu, hmmm kodai in tsananta bincike ingani meyasa suke kidnapping idan aikinsu kenan gara hukuma tasan da zamarsu idan kuma wata matsala ce ta damesu idan da hali sai intaimakesu. Zantukan datakeyi acikin zuciyarta kenan yayinda bacci yakauracewa idanunta. Haka taka sance harzuwa lokacinda shahararren 6arawonda yafi 'yan kidnapping iya sata yazo yayi awon gaba da ita wato bacci . Gajiya ne yamamaye mata jiki hakan yasa ta makara har karfe 6:30am bata tashi daga bacci ba mahaifiyarta ce taje ta kwankwasa mata kofa sannan tatashi tayi sallah daga bisani taje takarya kumallon safe, a6angaren su Rilwan kuma dasafe suka tashi sukaje suka hado kayan tea suka kawowa baaba jummai tahada musu mai kyau sannan suka karya, awannan ranar duk yaran gidan sun kasance cikin walwala kota ina tsalle tsallensu kawai sukeyi. Su Rilwan suka je suka sami baaba jummai sannan suka sanar da ita zasu fita aiki tayi musu addu'a sannan tace musu Allah yabasu sa'a suka amsa da ameen. Nanfa suka shirya suka fita batareda ma sunsan inda zasuje ba. A6angaren khairat kuwa bayan tagama hutawarta Abbanta yakira likita yace yaduba ta likita yagama bincike yace 'yarka lafiyanta lau babu abinda kedamunta. Madallah Alhaji ya amsa sannan yadubeta yace ke khairat dolenki ki amsa min wannan tambayar. Dasuka dauke ki ina suka kaiki kuma ya akayi suka saceki, atakaice kibamu labarin duk abinda yafaru daga farkon kamaki har karshe. Saita gyara zama sannan tace....... haka take ina mai baku hakuri yau bisa makara danayi wajen kawo wannan labarin hakan yafaru ne sakamakon ayyuka dasuka shamin kai..TAKE novels / HAKAN TAKE part 4 HAKAN TAKE part 4 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 16:43 bayan likita yatabbatar musu babu abinda ke damunta nanfa Alhaji Haruna yayi godiya ma likita sannan yasallamesa daga bisani yadawo yazauna tareda Mahaifiyarta, Alhaji yadubeta yace khairat ya akayi wannan abin yafaru dake inaso kibamu labari daga farko har karshe. Nanfa tagyara zaman sannan tadubesu tace Abba wallahi yarane kanana suka kamani. Bayan naje gidansu kawata maryam tayimin kitso ina dawowa ahanya sainaga wani akwance agefen titi kamar motace takadesa taki tsayawa nikuma dama abba kullum kuna cemin idan naga mutum acikin wani hali intaimakesa idan akwai hali, natsaya taimakonsa ashe lafiyansa lau kawai tarkone yahadamin nikuma bansaniba ashe sunada yawa kawai sai suka kamani suka rufemin idanu suka kaini wani wajenda bansani ba, nayita kuka sukyaleni amma sunki alokacin da umma ta kira wayana yana hannunsu sai bayan an kaimusu kudin sun dauka kafinnan suka daukoni amota suka kawoni bakin hanya sannan suka kwancemin idanu suka gudu. Hajiya ajiyar zuci tayi sannan tace toh ke meyasa bakiyi ihu ba alokacin dasuka kwance miki idanun Alhaji yace ai tayi kokarima data iya dawowa, tace umma wallahi yarane kanana . Alhaji yace akwai alama ai , Hajiya tace toh Alhaji yanzu dai sai ayi taka tsantsan da yarinyar nan kagani har anfara samun matsala, Alhaji yace kwarai kuwa daga yanzu babu inda zaki na zuwa daga makaranta sai islamiya shidinma zan hadaki da driver yarika kaiki. Ta dan saki baki cikin shagwa6a abba babu abinda zai sake faruwa dani, ke rufemana baki ummarta tadaka mata tsawa , tatashi cikin fushi dagudu tanufi daki ta haye kan gado tana zubarda kwalla. Biyota Hajiya tayi tareda fadin bazaki shirya kitafi makaranta bane kuma? Sai alokacin ta tuna taduba agogo karfe 7:20am dasauri ta tashi tashirya tadauki jakarta sannan tafito Alhaji yace kije driver dina yakaiki kafinnan asama miki driver, bata ce uffan ba tafito aka kaita makarantar tana zuwa kai tsaye tawuce wajen maryam kawarta ya akayi tace lafiya sai yanzu kike zuwa? Tace eh hmm kinsan me? Maryam tace a'a sai kin fada tace akwai labari amma sai anfita breakfast. Bayan antashesu breakfast ne suka zauna A'isha takwashe labarin abinda yafaru da ita jiya ta zantarwa maryam saidai ta6oye mata wasu abubuwa, Suka danyi dariya da raha irinnasu na kawaye sannan suka koma aji. A6angarensu Rilwan kuma bayan sun fito ne suka zauna suna shawarar abinda yakamata suje suyi awwal yace tunda akwai kudi awajenmu har dubu 180 mezai hana munemi wani abu kawai mufara sayarwa, sagir yadubesa toh kai aganinka meyakamata mufara sayarwa ne? Rilwan yace duk abubuwan suna da tsada kuma babu riba kanaga ko pure water bazamu saya muna sayarwa ba awwal yafada yayinda ya kura musu idanu, hmmm magana kawai kakeyi sagir yafada kai kasan pure water sai mai sanyi ake saya mukuma bamu da fridge dinda zamu saka aciki yayi sanyi, hakane Rilwan yafada sai mai sanyi ake saya, Sagir yace kai bross inaga fa babu sana'a mai kawo kudi sosai kamar kidnapping kodai zamu hada kayan aiki ne kawai mushiga harkan gadan gadan, hmmm akwai hadari fa dan wataran za'a iya harbemu idan kuma aka kashemu suwaye zasu kula da kannemmu marayunnan? Rilwan yafada cikin tambaya. Hmmm toh meyasa bakayi wannan tunanin ba alokacin da muka shirya zamu sace khairat, ai wancan lokacin hankali na ba'a jikina yake ba. Yanzu bana bukatar wancan aikin koda satar ma zanyi saidai na nemi wata hanyar amma badai kidnapping ba? Awwal yace meyasa kace haka? Hmmm baka sani bane jiyannan bakaramin kamewa nayi ba alokacinda kuka tafi kuka barni daga ni sai ita nakare mata kallo gaskiya komai ta hada shedan yaso yashiga zuciyata amma Allah ya kiyaye, Sagir ya tuntsire da dariya ashe bani kadai bane naji abin, Awwal yace nine kadai banji komai ba, Rilwan yace masa karya kake makaryaci ai kaidin ba waliyyi bane kai ko waliyi ne kai ka karema khairat kallo sai kaji wani abu na yawo a kwakwalwarka balle ma kaidinne bamu sani ba?. Suka kwashe da dariya, yanzu ba wannan ba me ake ciki? Sagir yakatse musu zancen dasukeyi hmmm kagane inaga zaifi dacewa ko wanne daga cikinmu yaje yanemi sana'a ko wanne iri ne idan wannan yakawo wannan yahado can sai mu tara awaje guda ko ya kuka gani? Awwal yafada Rilwan yace sam haka kuma baidace ba, yanzu ba tunda muncewa Baaba jummai leburanci mukeyi kawai muje muyi ? Hmmm a'ina kakega zamu sami leburancin Sagir yajefa masa tambaya. Hmmm wannan kuma me sauki ne idan muka fita bayan gari ga masu gini suna neman 'yan aiki basai muje muyita mika musu kasa ba naji ance akowanne wuni naira dubu biyu ake biyan kowanne lebura Awwal yafada, kai naira dubu biyu? Rilwan yatabaya cikin mamaki awwal yace kwarai kuwa , suka danyi shiru suna nazari karshe dai suka yanke shawaran zuwa bayan gari domin su nemi aikin gini, wani waje sukeje inda ake gina wani offstaire ana hawa na daya nanfa suka tambayi aiki aka karbesu batareda sun shirya akan kudin da za'a sallamesu ba, haka suka hau aiki dauko blocks sukeyi daga kasa suna kaiwa sama suna ajiyewa, kafin aje ko ina mutanenka suka fara sarewa, suna cikin aiki Rilwan yadauko blocks har ya kusan haurawa blogs din yakufce ahannunsa nanfa manager din ginin yace masa yawwa kafasa ko toh acikin kudin aikinka za'a cire kudin block dinnan Naira 60 ne, kaman zaiyi magana sai kuma yafasa haka yaci gaba da aiki misalin karfe 12:00 pm yunwa takamasu Sagir yaje yasami manager yace Ranka dade yunwa mukeji abamu acikin kudin aikinmu musayo abinci, mutumin yakallesa yace akanme za'a baku kudi bayan baku gama aiki ba? Awwal yataso Haba ranka dade aikin nan fa bazaiyiwu da yunwa ba yakamata abamu ko kadanne ba lalle ne kudin aikinmu duka za'a bamu ba. Yadubesu yace toh baza'a baku din ba, idan baiyi muku ba kubar aikin Rilwan yana sama yaji manager yana zance sai yakuma sake block din dake hannunsa har kasa block din yakuma fashewa, manager din yadaga kai yakallesa tareda fadin kai bakada hankaline Rilwan yace eh banda hankali din yana saukowa yana kallon manager idanunsa sun sauya zuwa jajaye yayinda dazarar kagansa zaka gane cewa ransa a6ace yake, idan kasan wulakanci zakayi mana meyasa kadaukemu aiki? Ai gara kace bazaka daukemu ba akan irin wannan. Ran manager a6ace yace toh sai ku bar aikin ai dakarfi yayi zancen, awwal ma yadaka mai tsawa toh sai a sallamemu kudin aikin mukayi. Sauran masu ginin suna gefe suna kallonsu hmmmm yau manager yahadu da marasa kunya irinsa wani magini yafada yayinda yadubi dan uwansa. Ah duniya ce ai dama bazaisan muna hakuri dashi ba sai yadauki wasu gashi yanagani ai dayan yabashi amsa, manager yadubesu yace aikin nawa kuka yine? Duka duka dubu daya muke biya 6 to 6 ku kuma bakuzoba sai kusan karfe tara yanzu kuma bai wuce karfe sha biyu ba sabida haka kowannenku naira dari biyu za'a bashi kai kuma dama kafasa blocks guda biyu sabida haka zan cire kudin blocks din kowanne block naira 60 ne kafasa guda 2 yakama naira 120 kenan za'a cire acikin dari biyun daza'a baka yanzu kudinka zai kama naira 80 kenan, kuttt manager ai ko uban kane fir'auna wallahi karya kakeyi Rilwan yafada , kowannenmu dubu daya zaka bashi idan bahaka ba wallahi duk ginin da akayi damu sai mun hau mun rusa , Awwal yafada afusace, toh bismillah kuje kurusa dan Allah manager yafada ransa a6ace kawai sagir yahaura dagudu yaje yarinka dukan gini dakafarsa kafin ka ankara 6angare daya ya abko kasa sauran leburorin dasuka ga haka nanfa suka zo suka rike Sagir. Bakada hankali ne wani katoto acikinsu yafada yayinda yadamke hannun Sagir awwal yajuyo yakallesa sannan yace wannan ai mahaukaci ne bakaga shi bai ce komai ba sai 6arna shi dama haka yake idan ransa ya6aci. Ok toh kar yakara zuwa nan wajen wancan yafada sannan yakarisa inda manager yake yayinda manager yacire wayarsa yakira 'yan sanda alokacin sukazo suka tattare su Rilwan basu tsaya ko ina ba sai police station, bayan sunje aka tambayesu suka fadi duk abinda yafaru sannan suka sanar da cewa su marayu ne kuma sunje neman na abinci ne suna jin yunwa yahanasu kudi sannan kuma yana nema yacucesu, yan sanda suka bawa kowa rashin gaskiya sannan suka tambayi su Rilwan ko akwai kudin da zasu biya ginin dasuka rusa nanfa sukayi kememe tareda cewa basa maganin ko sisi haka 'yan sanda suka bawa manager hakuri sannan suka gargadi su Rilwan karsu sake komawa.ovels / HAKAN TAKE part 5 HAKAN TAKE part 5 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 16:45 nanfa aka sallami su Rilwan tareda sharadin karsu sake komawa shikuma manager aka bashi hakuri. Nanfa 'yan sanda suka sallamesu daga case din, gabadayansu suka fito ransu a6ace manager yana kallonsu suna kallonsa yadubesu yace lalle kuwa yarannan bakusanni bane Allah yakiyaye kushiga hannuna wallahi zaku dandana kudarku. Awwal ya tuntsire da dariya sannan yace lalle kuwa kayi mana bahaguwar fahimta amma kasake tunani tukunna wannan abinda mukayi maka ahakanma a masana'antarka ne kuma muna tsoron idanun wasu leburorinka amma idan kayi musu ka gwada nemanmu da wata matsalar kagani. Ransa a6ace yashiga cikin motarsa yatafi, suko su Rilwan suka kama hanyar gida suna tafiya suna ta sam6atu, sai Sagir yace yanzu idan munkoma gida me zamucewa baaba jummai? Shiru suka danyi sannan awwal yace wannan ai abu ne mai sauki dama ai munada dubu dari da tamanin canjinmu daya rage, toh aciki zamuje mu dauki dubu goma sai muce mata mundawo ne daga aiki yau muntashi dawuri, eh toh ni inaga kyanta idan mukaje mufada mata gaskiyar abinda yafaru damu yau Rilwan yafada . Sagir yadan jaa lumfashi sannan yace toh kungane abinda yadace muyi ayanzu kawai idan mukaje zamu sanar da ita yadda akayi sannan kuma zamu je mudau dubu goma mu nuna mata sannan musanar da ita abinda yafaru. Eh tabbas haka za'ayi. Suka ajiye zance har suka iso gida suna maganar manager. Shigarsu keda wuya dukkannin yaran dake gidan suka zo musu oyoyo suka rakasu har 6angarensu bayan sunje sunhuta sai ga Aisha takawo musu abinci. Goood Rilwan yafada tareda cewa Allah yamiki albarka , tace ameeen sannan ta'ajiye musu abincin tace yawwa yaya Rilwan har kun dawo yau? Yace eh wallahi yau dinne mun hadu da wani karfa ne yakawo mana cikas shiyasa muka dawo yanzu. Tadanyi murmushi sannan tace yaya yaufa jikin baaba jummai yatashi sosai wallahi harma dakyar take magana. Habadai? Har bata iya magana mai kyau? Awwal yafada hankalinsa adan tashe . Kwarai kuwa Aisha tafada yayinda ta gyada kai. Alaman eh. Toh waye yagirka wannan abincin sagir yatambaya. Nice nagirka tabashi amsa. Hmmm gaskiya muje mudubata kafin muci wannan abincin. A'a yaya dan Allah kutsaya kuci abincin tunkunna idan kungama sai kuje kudubata nasani yanzu haka kuna jin yunwa sosai kuma idan kukaje wajen baaba jummai bazaku dawo yanzu ba. Gara kuci abincin idan kungama sai kuje dubata. Hmmm kedai kawai kice kinaso aci abincin dakika girka ne , awwal yafada tareda murmushi. Hmmm tsaya wata zance nikam cin abincinnan zanyi yanzu sagir yafara jefa kuri'a. Nanfa sauran suka mara mai baya. Bayan sungama cinyewa Ai'sha tace ya kukaji abincin dana girka , awwal yace au ashe fa ke kika girka ko? Toh gaskiya baiyi dadi ba yafada ransa ahade. Cikin 'yan kankanin lokaci idanunta suka sauya, yaya Rilwan baka ji abinda yaya awwal yake fadamin ko? Hmmm manta dashi ai ko sarauniyar girki ta duniya idan taci wannan abincin sai ta koka. Tasaki dariya dakarfi cikin zumudi tatashi tayiwa awwal gwalo sannan tadauki kwanon abincin ta tafi dashi, su ko suna gamawa suka tashi suka nufi dakin baaba jummai sallama sukayi sukaji shiru suka karisa ciki suna ambaton sunanta baaba ! baaba!! Jikinne kuma? Gyada kai tayi alamar eh, Rilwan yayi ajiyar zuci sannan yakaremata kallo tabbas baaba tana cikin jinya wanda idan ba mutum ya kula ba bazai gane ba. Yafada yayinda ya waigo yakalli 'yan uwansa. sagir yace kamanya kenan? Yakamata Haba kagane mana tunda muke tareda baaba jummai duk rashin lafiyarta idan mukazo gaidata sai ta maida mana da zance. Gaskiya ne wannan , awwal yaja dogon lumfashi hankalinsa yafara tashi bisa yadda yaga suna zancen batareda tace ko uffan ba ko tanuna wata alama dazai tabbatar da karfin gwiwa ba. Kar mutsaya wani jira abinda zamuyi kawai shine mudauketa mukaita asibiti domin kuwa wannan matar uwarmuce aduk duniyarnan bamusan wata kamar taba tunda muna da dan guziri kawai mudauketa zuwa asibiti, suka nemo mai motar haya suka kaita asibiti. Nanfa likita yagwada ta yatabbatar musu dacewa akwai wani kurji daya fito mata agefen kodarta wanda tilas ne ayi mata operation sannan kuma acireshi da gaggawa idan kuma akasami jinkiri zai iya affecting din kodarta kuma takan iya rasa ranta matukar ba'a dace ba. Hankalinsu gabadaya yayi matukar tashi Rilwan yadubesa yace likita tunda abinnan haka yakasance kaga mudinnan da kake gani mu marayu ne gabadaya, wannan matar itace kadai taragemana ita ma babu dangi tsakaninmu da ita haka tarene mu harmu ka kai yadda muke ayanzu likita intakaice maka daga gidan marayu muke daga gwamnati har attajirai kowa yayi watsi da rayuwarmu itace kadai tabamu kulawa. Dan Allah likita kataimakemu nasani wannan aiki ne mai tsada amma kayi hakuri kasassauta mana kudin biyan wannan jinyar, likita yadanyi shiru sannan yayi dariya yadubesa yace my friend irin wannan ba sau daya ba basau biyu ba nasha haduwa da irinhaka tun ina taimakawa har nazo nadaina. What i want you to know arayuwar mu tayau babu wani maraya sai rago . Yo gwamnati ma ta fita daga lamarinku balle wasu kunga kudin aikin daza'ayiwa wannan matar Naira dubu dari biyu da hamsin ne acikin kudadennan ko naira bazan rage muku ba. idan zaku kawo kudi za'a yi mata aiki idan kuma kudi basu shiga hannunmu ba sai dai kuzo kudauki gawarta, anan kuma sai kun biya mata kudin gadon asibiti datake kwance akai. Haba likita kayi hakuri dan Allah kasassauta mana zamu baka dubu dari da tamanin awannan aikin Awwal yafada cikin kaskantaccen yanayi. Hmmm babu wani zancen dazan sakeyi daku kawai kuje kunemo kudi. Rilwan yatashi yakirasu yace inaso zamuyi shawara yadubesu gabadaya sannan yace 'yan uwa kungi dai yadda rayuwa takeson kifewa damu inaga mutuwar baaba jummai tamkar rasa rayuwanmu gabadaya ne , idan muka biye zance zance mukan iya yin jinkiri har asami akasai abisa wannan abin . Yanzu ya kuke gani za'ayi. alokacin hawaye suka fara kwaranya daga idanun Aisha takallesu daya bayan daya sannan tace yaya dan Allah ayi mai yiwuwa shin akwai hanyar daza'a samo kudadenda likita yafada? sagir yace Aisha kiyi hakuri yanda kikeji muma haka mukeji gaskiya bamu da hanyar samun dubu dari biyu da hamsin atafiyar da ake cikinnnan. Toh naji kayi zancen dubu dari da tamanin idan ance abada hakan tawace Hanya zaka samosu. Ai ayanzu haka munada dubu dari da tamanin wanda muka samoshi ta hanyar da baidace ba ke 'yar uwanmu ce sabida haka kinkai matsayinda bazamu 6oye miki komai ba. Rilwan yafada tahanyar kidnapping muka samo wadannan kudaden, what yaya mekace kidnapping?sace mutum ayi garkuwa dashi kenan fa? Kwarai kuwa ya amsa mata munyi hakane sabida magance matsalar yunwa data addabemu kuma gashi munyi nasarar hakan. Toh matukar baaba zata sami lafiya kota wannan hanyar zamubi munema mata magani. Tabbas hakane wannan Awwal yafada. Aisha abinda nakeso dake kawai kikasance tareda baaba mukuma zamuje munemo kudi kota wanne irin hali ne. Bata iya cewa komai ba kawai Rilwan yafice sauran suka bishi abaya hmmm lalle ma kuwa tabisu dakallo sannan tace Allah ya kiyayemin ku. Jim kadan suka dawo wajen likita da dubu dari da hamsin acikin kudin dasukayi kidnapping na khairat suka bawa likita tareda rokanshi akan cewa zasu kawo masa sauran kudin abinda suke bukata yagaggauta ceto rayuwar baabarsu , likita ya amshi kudade sannan yafara shirye shiryen aiki. Suko suka fita sai suka rasa inda zasuje su samo sauran kudin. Wata bishiya suka samu suka zauna akarkashinta Rilwan yace dan Allah muhadu muyi tunani wani attajiri ne yakeda kudin gaske wanda zamu iya sace 'ya'yansa har musami kudade awannan garin? Hmmm suka danyi shiru suna tunani karar wayar Rilwan ne takatse masa tunaninsa yadauki wayar dasauri ganin bakon lamba yana dauka yaj muryar Aisha tanacewa yaya Rilwan Baaba tana magana kuma tace tanason ganinku ayanzu yanzunnan take Rilwan yaji hanjin cikinsa sun fara kadawa. Hmmm toh gamunan zuwa yafada sannan yakatse kiran. Me yafaru Sagir yatambaya , akwai matsala Baaba tanason ganinmu ayanzu haka, gaskiya jikina yabani cewa ,, sai yakasa karasar da zancen kawai kuka yakufce masa. Hankalinsu awwal yatashi me jikinka yabaka awwal yafada yayinda shima yafara zubarda kwalla. Sagir yace kodai anfada maka rasuwa baaba ne? Rilwan yace a'a kawai kutashi mutafi yatashi yakama hanya suka bishi abaya awwal yana ta tambaya me aka fada maka awaya amma Rilwan yaki sanar dashi. Suka shiga asibitin agigice suka wuce kai tsaye har dakin da aka kwantar da Baaba jummai alokacin da sukaje likitan yafita daga dakin bayan yagama bata washi magunguna da allaurai zaifita suka cikaro dashi akan hanya , yawwa kun kawo sauran kudin ne ? Tambayar da likita yayi musu kenan. Hmmm kawai Rilwan yaja iska sannnan ya ture likita gefe yawuce ciki sauran suka mara mishi baya. Tana ganinsu ta tashi ahankali kamar ta fara samun lafiya. Sannu baaba suka fada. Yawwa ta amsa Aisha tafada min cewa kun bawa likita kudi kuma kuntafi neman wani kudin suka amsa kwarai baaba , abinda nakeso daku kuje kusami likita yabaku kudinku nikam ajiki na nakeji zanbarku ayau, nagargadeku da duniya ku guji tauye hakkin 'yan uwanku marayu inayimuku wasiyya da neman naku nakanku, sannan tamaida kanta takwanta gabadayansu suka fashe dakuka baaba kibar wannan zancen bazaki mutu yanzu ba sai kinga aurena baaba. Aisha tafada yayin matsanancin kuka yakufce mata. Batareda ta bata amsa ba tadanyi murmushi dukda cewa dukkan sassan ga6o6inta adaure suke amma hakan bai hanata nuna fara'a adan wannan lokacin ba. Ina mai gargadenku da ku hade kanku sannan ku kula da kannenku marayu. Dukkan yaran nan dake gidannan yanzu kula dasu zai rataya awuyanku. Kuma zaku yi hakanne sabida Allah, zanso ace marayun danayi raino tun suna kanana wasu tun ajarirai yau gashi sun girma har suna rainon wasu . Sabida haka kutaimaki maraya aduk inda kuke wannan shine iya abinda zan iya fadamuku. Kawai sukaji ta katse zancen takoma kalmar shahada tanayi tana maimaitawa har zuwa lokacin da bakinta yakafe idanunta suka tsaya farare suna kallon sama dukkan ga6o6in jikinta suka daina motsawa.vels / HAKAN TAKE part 6 HAKAN TAKE part 6 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 16:46 lokacin da bakinta yakafe idanunta suka tsaya farare suna kallon sama dukkan ga6o6in jikinta suka daina motsawa , wani ihu suka sake gabadayansu wanda sautinsa ya ratsa ko ina acikin asibitin haka yasa dukkan mutanen dake cikin asibitin hankalinsu yakoma ta inda karar yafito. Gabadayansu yarane babu mai bawa wani Hakuri Aisha tahau kan gadon tana jijjiga tana cewa baaba kitashi dan Allah baaba kar kitafi kibarmu acikin wannan rayuwar baaba. Alokacin likita yashigo jikinsa ahanzarce yadan tsaya yana kallonsu sannan yace look dan Allah kuyi hakuri bari nadubata, Rilwan yace haba likita wane irin duba ta kuma bayan kana gani har ta mutu? Ta mutu kuma? Likitan yatambaya Rilwan bai ko sake wai wayan likita ba kawai yasunkuyar da kansa kasa yana zubarda kwallla likitan yakaraso inda take kwance cikin sanyin jiki. Yakalleta tabbas wannan matar babu rai ajikinta yafada acikin zuciyarsa, yasaka hannunsa agefen wuyanta ya kuma cirewa, sannan yasauke kansa ahankali yadubesu daya bayan daya,hakane tarigamu gidan gaskiya yanzu kuka bashi ne mafita agareku ba kuje ku kirawo 'yan uwanku azo adauke gawarta sabida asamu akaita makwancinta. Sagir yadubesa yace likita bamu da kowa sai wannan tsohuwar daka gani, itama gashinan ta rasu yanzu yazamuyi waye mukasani zai taimakemu. Nidai iya zancen da zan fada muku kenan likitan yabude kofa yafita, Awwal cikin juriya yadubi 'yan uwansa yace duk garinnan babu wanda zai iya taimaka mana yanzu abinda zamuyi muje gidan babban limamin masallacin jumma'a musanar masa kukanmu kozai magance mana ita domin kuwa akwai motar makabarta amasallacin, hakane zancenka Rilwan yafada sannan yadubi sagir tashi muje gidan liman musanar dashi na tabbata zamu sami ganinsa suka je sukayi sa'a suka samesu nan suka kwashe labarinsu suka zantar mishi liman yayi kabbara sannan yashafa kansu cikin tausayawa yagayyaci mutane aka je aka dauki gawarta zuwa gidan marayu aka sallaceta sannan aka kaita makwancinta. bayan an dawo zaman kar6an ta'aziyya kowa idan yazo sai fatan rahama yake mata. Liman yakirasu yatambayesu ko sun san 'yan uwan baaba jummai dukansu babu wanda yasan 'yan uwanta , ita kawai suka sani kuma bata ta6a basu labarin 'yan uwanta ba. Liman yayi shiru yana dan tunani sannan yadubesu yace yanzu wazai koma kula daku kenan? Ajiyar zuci Rilwan yayi sannan yadubesa yace ranka yadade ayanzu haka bamuda wani gata sai Allah. Wannan matar da kake gani tun lokacin tsohon dan majalisan wakilai yadauketa amatsayin mai kula da dukkan marayun dake gidan yana biyanta Albashi har zuwa lokacin daya sauka tun daga lokacin take aikin Allah tana ciyar damu duk abinda muka ci ita ta bamu duk tufafin da muka sanya ajikinmu ita take saya mana , daga karshe duk 'yan kudaden da ta tara saida yakare tun tana bi tana naima mana taimako har tagaji tadena sabida irin wulakancin da akeyimata. Allah sarki liman yafada sannan yace Allah ya kara mata haske acikin kabarinta suka amsa da ameeen. Atakaice dai yanzu babu mai kulawa da rayuwar ku? Eh Babu suka amsa masa. Hmmm ranar jumma'a bayan mun idar da sallah zan bada sanarwa amasallaci ko Allah zaisa asamu masu taimakon ku, toh Allah yasa mudace suka amsa ameeen. Haka suka kasance cikin mawuyacin hali har zuwa ranar jumma'a bayan an idar da Sallah liman yatashi yasanar wa jama'a halin da yaran ke ciki sannan yayi karin bayani sosai tareda fadakarwa da kuma falalar taimakawa marayu . Yayi kira ga 'yan siyasa da attajirai abisa wannan lamarin sannan akayi addu'a aka zauna jira ko Allah zaisa wani yakawo taimakonsa amma shiru kakeji liman abin yayi matukar daga masa hankali gashi kuma shima bawani arziki garesa ba balle yataimakesu. Hakan yasa aka tara dukkannin kudin da 'yan agaji suka tara na fisabilillahi da ake tarawa amasallaci ake kaimusu shi duk kudin da ake tarawa yazama asusun gidan marayu , sannan liman ya umarcesu da suke zuwa wajensa suna daukan karatu haka zalika su nemi sana'ar da zasu rika juyawa Har Allah yakawo musu mafita sukayiwa liman godiya sosai, haka suka kasance amakon farko aka tattara duka kudin da aka samau amasallacin naira dari bakwai da hamsin da biyar(N755) aka kawo musu. Suka amsa hmm gaskiya wannan kudin babu abinda zai mana Awwal yafada sannan Rilwan yace ni kam tsaya tukunna akwai kudin mu awajen likita wanda muka kai za'ayiwa baaba jummai aiki dashi inaga da munje munkar6a idan yaso sai muyi kokari musami namu nakanmu dashi. Eh kwarai kuwa Sagir yafada , Aisha dake zaune tana gyara shinkafa tadubesu tace ai likitan can zaiyi wuya yadauki kudincan yamaida muku shi , sabida akasari jama'a yanzu duniya tarufe musu idanu , hmmm ke wannne irin zance kikeyi ne haka? Ai baiyi mata aikin da zamu bashi kudi har Naira dubu hamsin ba, Shin ko yasan ta wace irin hanya muka sami kudinnan ne? Har ga Allah bazamu kyale masa wadannan kudaden ba yanzu duka duka kudaden dake wajenmu Naira dubu goma shabiyar ne. Wannan ma Albarkacin kudin taimakon masallaci da liman yaturo mana ne. Hmmm ajiyar zuci awwal yayi yanzun abinda za'ayi anjuma mushirya mutafi asibitin muje musamesa bayun kudin aikin , toh inaga hakan za'ayi Rilwan ya amsa , bayan Alsha tagama musu abinci sunci sannan suka nufi asibitin kai tsaye office dinsa suka shiga bayan sun gaisheshi yadanyi musu jajen rashinta suka amsa, daga bisani Rilwan yafara jefa masa tambayar batun kudin, likita yadanyi murmushin munafurci sannan yace kudin ku ai anyi mata aiki dashi atunanin ku dama haka akeyi ne? Ai ba haka akeyi ba sabida haka kudinku anyi matsa aiki dashi. Kaga likita karkayi kuskuren raina mana hankali fa Sagir yafada ransa a6ace babu alamar aiki ajikin wannan matar har ta rasu abinda kayi mata bazai wuce Allura ba, sabida haka sai kabamu kudinmu wallahi, likita yadanyi ajiyar zuci sannan yacire farin glass din dake makale a idanunsa yadubesu daya bayan daya sannan yace kutashi kuficemin anan wajen idan ba so kuke acimuku mutunci ba? Kai likita dan Allah bama son wasa da hankali idan bazaka bamu kudinmu ba zamu iya kwata koda karfin tsiya ne. Kai ni kake fadama wannan zancen likita yatashi ransa a6ace kuficemin daga office marasa kunya banzaye shashashun yara ahakanne zakuce ku marayune kuna bakatar taimako? Waye zai taimakeku marasa kunya. Ahankali Rilwan yatashi yatsaya sannan yace zaka gani kuma zakasan kata6o maras kunya yadubesu kutashi mutafi, suka fita daga office din likitan Awwal yace haba bros meyasa kace mufita mukyalesa bayan kana gani irin rainin hankalin da wannan mutumin yayi mana yanxu kanaga yazamuyi musami kudinmu.? Ajiyar zuci rilwan yayi sannan yadafa kafadan awwal tareda cewa karka damu zamu kar6i kudin mu idan baiyi sa'a ba har da kari sai yayi mana akan kudinmu. Gidan sa zamuje cikin shigen 6arayi muyi masa dan karen duka sannan mukabi kudinmu . Hmmm kuna ganin hakan zaiyiiwu kuwa Sagir yatambaya, hmmm wannan ai mesauki ne kawai mukyalesa zuwa dare, suka sake dawowa gidan sai suka ga wata mota akofar gidan marayun yau kuma baki mukayi ne? Awwal yatambaya Rilwan ya amsa dacewa babu mamaki ko ansami wanda zai kawo mana taimako ne. Ko kuma acikin yaranmu dinnan wani danginsa sunzo neman sa, har suka iso bakin kofa suna sakar zance, bayan sunshiga ne suka ci karo dashi abakin kofa mar martaba ne hakimin gari yazo yakarema gidan kallo suna shigowa suka ci karo da dogarai suka durkusa suka gaisheda Sarki bayan sun gaisa sai yake tambayansu cewa kune manya awannan gidan ko ? Suka amsa eh yace toh Alhamdulillahi naji dadi dana kalleku haka. Ku manya ne kuma kungirma wanda har yakai matsayiin zaku iya rike gida batareda wata matsala ba sabida haka akwai abinda mukeso muyi awannan gidan muna so mukar6eta daga wajenku tunda dama ku ba cikakkun 'yan garinnan bane. Dan da ace akwai 'yan uwan iyayenku anan da tuni sun zo sun daukeku sabida haka abinda nakeso nasanar muku shine zaku je ku nemi gidan haya inda zaku zauna nan wajen zan gina wata cibiyar kasuwanci.. Nan take gabadaya Rilwan yaji yawun bakinsa yakafe wani abu kamar kullutu yamakale masa awuya shi bai wuce ba kuma bai fito ba kawai kasa fitarda zancen yayi bai sani ba ashe bashi kadai tashin hankalin ya ziyarta ba. Kawai jiyayi sagir yatashi da durkusawan dayayi tareda fadin; / HAKAN TAKE novels / HAKAN TAKE part 7 HAKAN TAKE part 7 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 16:48 sagir yatashi daga durkusawan dayayi tareda fadin haba ranka dade atunaninka idan kayi haka kayi mana adalci kenan? Karya kake dan talakawa tsintacce ba'a dagawa mai martaba murya sabida haka. Sarkin yadaga ma dogarinsa hannu yakatseshi alaman yadakata yatsaya jikinsa na 6ari kamar wani dan bori mai martaba ya karisa inda Sagir yake sannan yakallesa tareda dafa kafadansa ina tausayawa duk wani maraya , amma bana barin abinda zai sha bamban da yadda nashirya gudanar da mulkina . Kayi babban kuskure daka daga murya fiye da yadda nayi maka zance amma sabida tausayawan danake yiwa marayu zan kyaleka. Amma karka sake ko daga kai ka kalleni, haba mai martaba kafa san babu inda zamu je muzauna ya za'yi kazo mana da wannan zancen dan Allah mai martaba kataimaka ka kamanta adalci kamar yadda dogaranka suke yi maka kirari. Awwal yakatsesa da wannan furucin, jim yadan tsaya yana nazari sannan ya karkato da kansa yakallesa batareda yajuya dukkan sassan jikinsa ba, sannu gwani wajen sarrafa harshe toh dadin bakinka bazai samu shiga ba, abinda zan fadamuku nakarshe shine yau asabar zuwa rana ita yau nakeso afara gudanar da gyarace gyarace agidannan sabida haka kafin wannan lokacin kusan inda zaku koma ni babu ruwana, yajuya zai tafi Sagir yatashi azuciye yace sai muga wanda ya isa yazo yafitar damu awannan gidan, mai marata yatsaya ahankali yajuyo sannan yace kai sakarai idan kana ga kafadi abinda ranka yakeso dazu nakyaleka toh kasani fa yanzu bazan kyaleka ba yadubi dogaransa dake tsaye kukamashi kuyi masa bulala ashirin. Suka tinkaro babu jira Rilwan da Awwal suka taresu babu wanda ya isa yata6ashi awajennan dogarai ransu ya6aci kasancewar su biyu ne sunkasa ai watar da komai fada kawai suka barke da dogarai awajen, Aisha tana tsaye agefe sai kuka takeyi , maimarta daya ga abin zai gagara yaciro wayarsa yakira 'yan sanda tuni akazo aka tattaresu akaje aka rufe. Aisha kadai aka bari tareda sauran yara marayu su goma sha daya. Bayana ankaisu police station maimartaba yabada umarnin ayi musu horo nakwana biyu kada akyale kowa yazo dubasu sai lokacin yacika kafinnan asaurari case dinsu haka kuwa akayi ta gana musu azaba bayan kwana biyu aka fitar dasu sannan aka yanke musu sati daya sannan belin kowannensu naira dubu ashirin . aisha tazo dubasu suka sanar da ita hukuncin da akayimusu sannan Rilwan yayi mata kwatancen inda ya ajiye sauran kudinsu daya rage dubu goma sha biyar kiyi kokari ki cigaba da kula da yarannan har zuwa ranar da zamu fito idan akwai hali kije kafin ranar yacika kinemi gidan haya idan kinsamu sai kuzauna aciki zuwa ranar da za'a budemu sai kizo nan kisamemu kikaimu gidan ko kuma kizo nan kibamu address din gidan . Awwal yayi ajiyar zuci shin kanaganin zata iya wannan abin kuwa? Neman dakin haya agarinnan bakaramin abu bane mukaddara cewa kaine ina kasan zaka fara zuwa neman daki ? Rilwan yayi shiru yana nazari wani irin hawaye mai radadi suka zubo daga idanunsa gabadayansu sai suka kama kwalla. Sagir yace yanzu yaushe muka san ranar fitarmu anan bayan kafin a sakemu sai an bada belin kowannenmu. Karka damu zasu gaji da adana mu suda kansu zasu sakemu Rilwan yamaida masa zancen, 'yan mata kiyi hakuri lokacin mayardasu ciki yayi wani gandiroba yafada yayinda yakalli Aisha wani kuka yakufce mata innalillahi wa'ina ilaihi raaji'un tafada sannan tadaga hannunta sama ya Allah kana ganin Irin kuncin da muka shiga Ya Allah kaine kadai gatanmu kai kadai zaka iya magance mana wannan matsalar . Tadubesu zanyi iya bakin kokarina kafin ranar dsaza'a fitar damu daga gidan. Karshen zancen da tayi kenan ta juya tafita. Suka bita da kallo dukansu babu abinda sukeyi face kuka. Aka mayardasu bayan ta fita taje wajen lauwali maishago wanda shagonsa yake kallon gidan marayun tasanar dashi halin dasuke ciki sannan ta rokesa dan Allah yataimaka yanema musu dakin haya koda guda daya ne kafin 'yan uwanta su fito, lauwali Hawaye ne suka fara zuba a idanunsa dakyar yasamu yadakatar dasu. Sannan yace zaiyi iya neman dazaiyi zuwa gobe haka lauwali yaje nan yaje can yanema musu gidan haya babu mutane aciki dayawa sannan yabiya musu kudin wata 6 tun kafin su koma, Aisha tayi masa godiya sosai lauwali yace babu komai ai maraya na kowa ne. Saura kwana biyu lokacin da sarki ya yanka musu agidan yacika, Aisha ta kintsa kayakin yaran gidan gaba daya ta wankesu tadauresu washe gari dasafe suka tashi suka fito da kayakinsu suka nufi gidan hayan da lauwali yakama musu tafiya yaran wasu sai tsalle tsalle sukeyi wasu masu dan wayon daga cikinsu kuwa kuka suke yi tun suna tambayarta ina su yaya Rilwan har suka daina. Alokacin da suka zo tsallake titi Aisha ta tsaya ta sauke kayanta sannan tace musu karko wani yaro yace zai tsallaka sutsaya zata tsallakar dasu takama hannun yara biyu Bilal da fatima tarike hannayensu tace sauran su jirata idan ta tsallakar dasu saita dawo takuma tsallakar da sauran haka kuwa akayi tana hayewa kan titi adaidai lokacin ta tsallake zuwa dayan 6angaren juyawar dazatayi kawai tagansu gaba dayansu sun biyota zasu tsallaka suma Innalillahi wa'inna ilahi raaji'un wata mota kirar golf ce tafito aguje tayi kansu gabadaya sai suka hadu awaje guda sabida su make ajikin juna bisa tsoro, kamar zatayi hauka take magana ku komaaaaa!! Amma ina hankalin yarinta bai basu daman komawa ba, haka wannan motar ta hankadesu gabadaya duka tayimusu. Kaca kaca suka watse agefen titi wani hannunsa tayi can wani kansa ta guntule wani kuma ba kafa wani kuma yaji@mugun rauni haka suka fadi su tara (9) wani irin Ihu tasaka batareda ta iya jan lumfashi ba ta yanke jiki tafadi akasa dukkan jama'ar dake wajen suka taru masu agajin gaggawa suka zo gabadaya aka daukesu alokacin kawai acikinsu yaran sai da aka fitarda gawaki 7 wadanda direct jana'izarsu akayi sauran yara biyun kuma aka daukesu kai tsaye aka tafi dasu asibiti tareda Aisha acan sauran ma suka karisa Aisha farkawar dazatayi sai kawai taganta akan gadon Asibiti ga lauwali mai shago sai kuma likita dayake tsaye akanta sannu ko likita yafada mata, ahankali tagyada kanta sannan tafashe da kuka ya ubangiji meyasa baka kaddara mutuwata awannan lokacin ba, na gwammace intafi barzaku kai tsaye akan irin wannan rayuwar hawaye masy radadi take ta yi. Lauwali mai shago yakariso inda take yadubeta kiyi hakuri Aisha kidauki wannan abin amatsayin kaddara duk abinda kika ga yafaru dake a wannan duniyar mukaddari ne daga Allah madaukaki shine kadai yasan dalilin yin hakan. Likita din yadubesa yace ahankali insha Allahu zata warware tunda har ta farka , lauwali yace nagode likita. Sannan likitan yafice daga dakin yabarsu lauwali yayi iya bakin kokarinsa domin yadanne hawayen da suke yunkurin sulalowa daga idanunsa amma abin yacitura dasauri yasaka hannun rigarsa yashare, meyasa kake kuka lauwali? Tajefa masa tambaya bai bata amsa ba yadaga kanshi sama nanfa ta tambayeshi ina kanne na? Hawaye suka kuma malalowa da idanunsa Allah yakarbi rayuwarsu gaba daya fatima da Bilal sune kadai suka saura yanzu haka suna gidana, kuka yazame mata tamkar abinci haka tayi kuka har ta gaji lauwali babu irin rarrashin da baiyi mata ba amma sai da tagaji tabari likita yashigo ahankali da wasu kayaki ahannunsa , akwai bukatar mukara mata ruwa leda daya hakan zaisa tasami karfin jiki likitan yafadawa lauwali ya'amsa toh likitan yace idan kanada uzuri zaka iya tafiya zuwa anjima sai kadawo yanzu tana bukatar nitsuwa yadda komai zai tafi cikin sauki lauwali yace toh Aisha bari naje shago naduba nabar yarona awajen tun dasafe tace toh lauwali maishago Allah yasaka da alheri ya .ameeen bayan lauwali yatafi likita yace mata kidena daga hankalinki kinji ko zaki samu lafiya nan bada jimawa ba. Sannan lilitan yafita yabarta ita kadai tana kwance tana zubarda kwalla har bacci yayi awon gaba da ita , Su Rilwan kuwa dub abinda yafaru basuda labari suna kulle agidan prison mako dayan har tawuce batareda Asha ta ziyarcesu ba wannan shine yatabbatarmusu cewa lalle kuwa duk yadda akayi akwai matsala, alokacin da bacci yadauketa sai kawai tafada cikin mafarke mafarke gatanan agefen titi tana ganin 'yan uwanta yaran da mota yakadesu gabadaya suna daga mata hannu tareda Baaba jummai dakuma yayunta Rilwan ,awwal da sagir dukansu sunata kiran sunanta, agefen titi Aisha ki tsallako mutafi gida abinda takeji suna fada kenan hakan yasa tayi wani kara mai karfi wanda yafarkar da ita daga baccin da tsalle tatashi ta cire ruwan da ake daura mata kawai tabude kofa tafito kanta babu dankwali , kafarta babu takalmi takama hanya gudu kawai takeyi har ta fita daga asibitin tanufi inda taga 'yan uwanta amafarki kamar wacce tayi sabon hauka duk wanda yaganta abinda zai iya fada mata kenan sabuwar mahaukaciya. Ta iso wajen ta tsaya atsakiyar titi tana waige waige tana kiran sunan 'yan uwanta, tareda fadin ina kuke gani nan nazo. Adaidai lokacin Alhaji Haruna tareda driver dinsa da khairat sun fito daga junction din dake wurin dakyar drivern Alhaji Haruna yayi control din motar duk dahaka saida suka kuskureta kadan anan tafadi kasancewar tasowanta kenan daga gadon asibiti shiyasa jikinta babu karfi. Dasauri sukayi parking agefen titi innalillahi wa'inna ilahi raji'un 'yar waye wannan Alhaji Haruna yatambaya, yayinda sukaje suka dauketa kamar jaririya kafin kace me jama'ar wajen suka taru adauketa aka sata cikin mota khairat tariketa suka nufi private hospital din Alhaji haruna kai tsaye,vels / HAKAN TAKE part 8 HAKAN TAKE part 8 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 16:49 farkawan da tayi sai kawai takalleta kan gadon asibiti tabude idanunta ahankali idanunta sukayi arba da wata budurwa mai kyau na kin karawa wacce bazata iya misalta ta ba, Sannu ko ta furta mata cikin tausayawa, uhm ta amsa sannan tace lauwali har yanzu baidawo bane? Khairat ta danyi shiru lauwali kuma? Ta tambaya Aisha tace eh lauwali maishago, ajiyar zuci khairat tayi sannan tace kikwantar da hankalinki zai dawo yanzu likita zaizo yaduba ki, takomar da kanta takwanta sai awannan lokacin ta kula ba ageneral Hospital takeba sabida kalan fentin asibitin daban yake da wannan ta daga kanta sama takalli fankar dake kadawa acikin dakin yasha bamban da wanda idaniyar ta suka saba gani, ina ne nan? Ta tashi ahankali tareda tambayar khairat tadanyi murmushi karki damu kawata nan asibiti ne, ya sunanki? Sunana Aisha. Ni kuma sunana khairat, awani unguwa kikeda zama kuma ke 'yar wayene, tana jin wannnan tambayar hawaye suka mamaye gurbin idanunta hmmm kafinta bude baki aka bude kofa likitan ne yashigo Alhaji haruna nabiye dashi abaya, yauwa tafarka ko? Eh abba ta farka khairat tabashi amsa yadanyi ajiyar zuci sannan yace likita meke damunta ne? Likitan yadubesa ranka dade yarinyar nan abinciken danayi asali batada lafiya dan ajikintama akwai alamun an daura mata ruwa da kuma allurai wadanda basu wuce 24hrs da akayi mata su ba sannnan kuma babu wani alamar buguwa ko jin ciwo atattareda ita ina kyautata zaton motarku bai ta6ata sosai ba, kwarai kuwa Alhaji yafada. Sannan yadanja lumfashi wannan kenan yanuna cewa daga asibiti take zata koma gida wannan abin yafaru, likitan yadanyi shiru sannan yadan jaa zance eh toh gaskiya yadda naga jikintannan zaiyi wuya ace daga asibiti take likitoci ko Nurses sukyaleta tafita ahaka bazaiyiwu ba sai dai ko wani abu ne yafaru, koma dai menene zamuji Alhaji yakarasa kusa da ita sannu ko ta dago kanta ahankali ta amsa yaa sunan mahaifinki khairat tace Abba nayi mata wannan tambayar amma sai kuka yahanata bani amsa, kuka kuma? Alhaji yakaraso kusa da ita sannan yace kikwantar da hankalinki 'yan mata kinji fada mana inda 'yan uwanki a ina suke yakamata susan abinda yake faruwa dake bude bakinta tayi danufin zatayi magana sai kuma takasa sabida wani abu data ji yana kokarin fizga acikin kirjinta, yadai kiyi magana mana khairat tazauna akan gadon sannan ta dagota tariketa kidaure ki amsa wannan tambayar likita na tsaye yakura mata idanu. Alokacin ta bude bakinta zatayi magana wani jini yaketo daga bakinta kamar an turoshi yawatse awajen kayan dake jikin khairat duk jinin ya6atasu likitan yakaraso wajen dagudu yariketa sannan ya umarcesu da ficewa daga cikin dakin suka fita ya gama operation sannan yayi mata alluran bacci yadubi Alhaji zaku iya tafiya kunga yanzu kusan karfe 8:0pm ake nema idan yaso gobe sai kudawo, khairat tace Abba zan dawo nan mukwana tareda ita duk wata kula da ita zanyi dafarko Alhaji yace sam bazaiyiwuba daga bisani ya amince khairat zata zauna sukwana awajen. Adayan 6angaren kuma alokacin da khairat tafita babu wanda ya ankara da fitar datayi sabida haka ma ba'asan tafita ba sai bayan sama da 1hr likitan yaje dakin danufin dubata yana shiga yaga wayam agigice yafito yana kiran nurse ina patient din dake wannan dakin suka zuro masa idanu kawai babu wanda ya bashi amsa likitan yafita hankalinsa yayi matukar tashi yafita daga cikin asibitin yana dube dube adaidai lokacin saiga lauwali yadawo akan mashin dinsa tun kafin ya iso yakalli likitan ya tsare hankalinsa gabada yakoma kansa, azuciyarsa yace anya kuwa lafiya har yakaraso inda likitan yake yana sassarfa aranshi kafin yakarisa tsayawa likita yace dan Allah yarinyar nan bata koma gida ba ? Nazo dubata naga dakin babu kowa aciki ko kunzo kun dauketa ne likitan yana zance hankalinsa atashe lauwali yace mekake cewa ne likita? Kana nufin bata asibitinnan yanzu kenan? Kwarai kuwa lauwali take zufa ta mamaye jamfar dake jikin lauwali a'a likita inaga kayi 6atan kaine mukoma musake dubawa likitan baiyi musu ba suka je dakin dankwalinta kawai suka gani awajen lauwali ransa a6ace yakalli likita haba malam wannan wane irin sakarci ne? Ya za'ayi ace har ta fita babu wanda yasan tafita balle asan inda taje? Likitan yace muje mutambayi mutanen waje ko akwai wanda yaganta acikinsu, suka fita suka sami wani mai sayarda lemu abakin kofar asibitin malam mustafa dan Allah bakaga wata yarinya ta fito nan babu dankwali akanta sannan kuma inaga babu takalmi? Eh tabbas nakalleta tafito tana gudu sosai ni nazata ko wani dan uwanta ne yarasu acikin asibiti shine tafito haka shiyasa ma banyi tunanin kamata ba. Innalillahi wa'inna ilaihi raaji'un lauwali yakama salati, likitan yace tun yaushe ne tafita mustafa mai lemu yayi ajiya zuci sannan yace gaskiya zai kai 1hr da fitanta idan ma baifi ba, hmmm lauwali da likita suka kama hanya suna tambayar mutane ko zasu cikaro da wanda yaganta kowa suka tambaya amsar da ake basu kenan wani yace musu yazata mahaukaciya ce, likitan yace ma lauwali abinda za'ayi yanzu mukai cikiyarta police station natabbata za'a ganeta, haka suka wuce kai tsaye zuwa station suka bada sanarwa, sannan suka tafi hankalinsu duk atashe likitan yakoma asibiti sabida yana da majinyata dayawa shikuma lauwali yakoma gida ko zai sameta agidansa amma shiru, awannan ranar aka fitar dasu Rilwan sannan aka sallamesu daga prison sabida gajiya da akayi da adana su batareda anzo anyi belinsu ba. Suna fita kai tsaye suka nufi gidan marayu alokacin gabadaya sun rame kamar basu ba duk abinda yafaru basu da labari isowar su sukaga anata gine gine awajen basuyi mamaki ba sabida sun san hakan zai faru abinda suke tunawa shine ina kannensu suka koma, Rilwan yakarisa wajen masu ginin yayi sallama suka amsa sai yaga kamar yaganesu, amma yamanta inda yata6a ganin wadannan mutanen, daga nesa yaji ana kunno masa ashar dubawan dazaiyi sai yaga manager din dasuka ta6ayin rikici dashi ne akan aiki, Rilwan yadanyi shiru yana kallonsa har zuwa lokacin daya kariso yau kuma me yakawoku wajena waye kuma yagayamuku muna aiki anan, kuna tunanin zan daukeku aikine ko kuma kunzo bani hakuri ne? Yakarisa maganar tareda rike kunkumi, hmmm malam muba wannan yakawomu ba ina mutanen da ke cikin gidan Awwal dake gefe yamaida masa zance , wannan kuma bansani ba sai kunemi wanda zaku tambaya nan gidan marayu ne kuma tun kafin mufara aiki sun tashi sun bar wajen, ina kuma suka koma dan Allah Sagir yafada yayinda yake kallon manager ,yajuyo yakalli sagir yakare masa kallo sai yatuna asarar da yata6a yimasa sai yace mahaukacin banza waye zai baka amsa sai kaje kanemi mahaukata 'yan uwanka su amsa maka tambayar, Rilwan yadanyi kasa da murya yi hakuri manager dan Allah ina suka koma? Toh nidai bansani ba yafada ransa a6ace yajuya yabarmusu wajen, Rilwan yace bari muje mutambayi lauwali mai shago wata kila zaisan inda suka koma. Suna zuwa kofar shagonsa lauwali yagansu kamar amafarki haaaa Rilwan,Sagir,Awwal sannunku da gajiya yadauko kujeran zama yabasu sannan yadauko biscuit da maltina yabawa kowannensu jikinsa amace yazauna akusa dasu ya gama fahimtar cewa lalle kuwa basuda labarin abinda yafaru bisa dukkan alamu. Yana zaune Rilwan yatambayeshi malam lauwali ko kana da labarin inda kannenmu suka koma? Kugama cin abincin tukunna zan kaiku. Bayan sun gama lauwali yatsayarda mai adaidaita sahu basu tsaya ko ina ba sai gidansa suna sauka fatima da Bilal suka zo dagudu suna kuka suka rungumesu awwal yatsaya yadanyi shiru yakalli Bilal ina sauran yatambayesa ai mota yabugesu sun rasu kai tsaye kawai yabawa Awwal amsa what Awwal yafada me kace Bilal lauwali baiso asanar dasu awannan wajen ba yafiso sai sun shiga gida sun sami nitsuwa tukunna, Sagir yace bangane sun rasu ba yadaga kai yakalli lauwali sai yaga hawaye na sauka daga idanunsa, ina Aisha ? Rilwan yatambayi Fatima batada lafiya itama tunda safe kuma muke nemanta bamu ganta ba fatima tabashi amsa, yayi ajiyar zuci kasancewar yaji Bata mutu ba, lauwali yadubesu yayinda kowannensu yafita daga hayyacinsa dan Allah kushigo daga ciki inaso muyi magana babu musu subaka bishi ciki yadauko musu taburma ya shimfida sannan yabasu labarin abinda yafaru daga farko Har zuwa lokacin da suka nemi inda Aisha tashiga suka rasa, sukayi iya kukansu suka gaji sukayi shiru sannan ne Awwal yace gaskiya nikam bazan iya zama awannan garin ba ko ni kadai zan tafi haba Awwal ina zakaje idan kabar wannan garin? Lauwali yajefamasa tambaya, hmm wajajen zuwa suna da yawa nima bazan zauna anan garin ba Sabida zalunci yayi yawa Sagir yafada cikin bacin rai hmmm zaku iya tafiya ko ina ne amma zan baku shawara kar ku ta6a haduwa awaje daya kawai kowa yaje yanemi nakansa domin haduwa awaje 1 yana yawan kawo mana akasi tareda aikata abinda baidace ba. Nima karshenta barin garin nan zanyi Sabida nasani wata rana zan iya kaiwa Sarki farmaki kuma idan akayi rashin sa'a zai iya mutuwa nima kuma nasan kasheni za'ayi subhanallahi lauwali yafada batun kisa fa kakeyi Rilwan uhm kwarai kuwa malam lauwali har ga Allah abinda maigari yayi mana yacancanci mutuwa idan zakayi duba rayuka nawa muka rasa sabida korarmu dayayi agidan da muka taso muka sami kanmu aciki. Ajiyar zuci lauwali yayi sannan yace toh bakomai zaku iya tafiya neman kudi tunda jama'a dayawa suna fita cirani kuma suje susamo rabonsu bisa dukkan alamu yafadi zancen ne kawai sabida yaji Rilwan ya ambaci kisa. Hmm amma dole ne fa zamu nemi Aisha kafin mutafi idan mukayi kwanaki 2 bamu sameta ba zamu iya tafiya Allah shi kadai yasan dalilin hakan. Shikenan suka ajiye zancen, sabida lokacin Sallah yayi suka fita sukayi sallah sannan lauwali yakaisu gidan hayan da ya kama ma kannensu danufin zasu koma sai Bilal da kuma Fatima lauwali yace yayi alkawarin rikesu zasu zauna tare da yaransa, bayan sun je sun zauna Rilwan yake cewa yanzu fa bamuda kudi ko kadan idan ma zamu tafi ina zamu sami kudin mota. sagir yace yawwa katuna min yau yakamata muje mukar6i kudinmu dake wajen likitan da yayiwa baaba jummai aiki. Hmmm kwarai kuwa Awwal yafada sannan yace dama mun ajiye zancen zamu je mukar6i kudin kota wane irin hali amma yanzu ya kuke gani hakan zaiyiwu kuwa, kamar yayiwu ma inji Rilwan aini yanzu babu sassauci tsakanina da duk wani azzalumi acikin wannan garin wallahi idan bai bamu kudinmu ba sai na sauke takaicin dake damu na akanshi, kaga dai gardaman dayayi mana inji awwal, kukyalesa cikin dare zamuje masa da misalin karfe 1 na dare , hmmm kana nufin zuwan 6arayi zamuyi kenan awwal yatambaya? Eh mana idan bahaka mukayi ba toh wallahi akwai matsala dan bazai bamu kudin nan ba. Amma fa muna yawan sa kanmu cikin tsautsayi, awwal yafada cikin sanyin jiki kaga idan bazakaje ba ko mu biyu zamuje , kabi kanata sarewa baka ganin irin yadda aka zaluncemu agarinnan daga nan ma zaka gane cewa ita rayuwar nan idan baka zama jan wuyaba toh wallahi dolenka kazamo abin tausayi gara kawai yazama ana atare atare dani akan yazama ana tacemin Allah sarki sagir yazazzago ma awwal zance. Naji zanje awwal ya amsa. TAKE novels / HAKAN TAKE part 9 HAKAN TAKE part 9 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 16:50 Misalin karfe Shabiyu nadare suka shirya cikin bakaken riguna suka fita kai tsaye suka je gidan likitan, bawani babban gida bane sabida hakane ma babu mai gadi saidai kofar gidan arufe, Sagir yakama katangar gidan yahau yatsallaka Sannan sauran suka biyo bayanshi, kai tsaye suka wuce cikin parlonsa alokacin misalin karfe 12:30 har bakin kofar dakinsa suka tsaya sannan suka kwankwasa, waye yatambaya suka yi shiru babu wanda yakuma motsi sai yataso danufin yaduba ko wanene yadauko takobi ahankali yana fitowa yana ready bakin takobin ne yafara fita kafin nan yambiyo baya ji yayi kawai an rike kan takobin dga gefensa na hagu anyi ciki dashi Rilwan yashigesa da kokuwa ya saukeshi da kasa Sagir yakwace takobin dake hannunsa din. Arazane yadaga kai cikin dimaucewa yakama zance wayyo dan Allah kuyi hakuri suwaye ku? Rilwan yasa hannu yacire bakin kyallen daya rufe fuskarsa dashi sannan yadubesa ina fatan kagane ko wanene ni? Cikin kidimewa yace wallahi banganeka ba dan Allah kuyi hakuri matarsa tataso ta durkusa agaban Rilwan dan Allah kuyi hakuri karku kashemin miji wallahi shikadai nakeda, ahankali Rilwan yajuya yakalleta jikinsa yadanyi sanyi yayinda ya tuna lokacin dasuke fadama likitan yataimakesu Baaba jummai ita kadai ta ragemusu. Ajiyar zuci yayi yadubi Sagir yayinda Yarike takobin ahannunsa yatsare tamkar wani mayakin tarihi. awwal kuma yatsaya abakin kofa Rilwan yadan dubeta cikin nitsuwa karkidamu babu abinda zamuyiwa mijinki amma fa sai munsami abinda mukazo nema ina fatan akwai kudi ko? Bakinta na rawa tace eh akwai Rilwan yace jekidauko yadubi auwal sannan yayi nuni da inda take alamun awwal yabita taje tabude wardrop tadauko wani jaka tazige zip din sannan ta durkusa tamikawa Awwal yakarba sannan yakara jan zip din yakuma kullewa uhm ya jijjga jakar sannan yadubeta Wadannan kudin sunkai Nawa? Bansani ba tafada hankalinta atashe uhm Rilwan yadubesa nawane kudin? 1.5million naira ne aciki kudin ma aikatan Asibiti ne wanda nakarbo daga banki dan Allah kutaimaka karkusa adaureni, uhm ashe kana tsoron dauri ko? Hmmm karka damu fa likita gidan yarinnan babu wani wahala sosai kawai wannan kyakkyawar matar takace zakayi missing dinta na wasu 'yan lokuta, bari murage maka asara Rilwan yaja bakin zip din yabude sannan yafitar da kudi fiye da rabi ya watsar masa awajen sannan yadubesa yace ramakon gayya tafita gayya dadi dukda cewa kace baka ganeni ba amma karbi wannan takardan zakaga ko su waye mu aciki. Rilwan ya jefeshi da wani dunkulalliyar paper sannan suka fita cikin hanzari suka bar gidan fitarsu keda wuya likita yatashi fuskarsa cike da damuwa yayinda matarsa take zubarda kwallla, tana jira taga me aka rubuta acikin wannan paper, wannan bakomai bane daga cikin sakayyar ubangiji. Mune yaranda muka kawo wata tsohuwa asibitinku ka juya mana fuska sannnan kaki duba mana marasa lafiyarmu har saida muka kawo maka kudi. Mune wadanda muka kawo maka dubu dari da hamsin kudin jinyar baabarmu kahau kan kudin sannan kuma kaki kayi jinyarta daga karshe rasuwa tayi, mune wadanda ka jefa cikin rayuwa ta jimami da kuma kunci ta sanadiyyar rasa uwarmu damukayi bisa sakacin dakayi. Mune muka zo wajen ka kadawar mana da kudinmu kahanamu sannan kace mudauki duk matakin da duk mukaga zamu iya dauka. Toh wannan shine matakin da muka dauka. Anan yazo karshen rubutun dake ciki pepar yadanyi shiru sannan yakalli matarsa ta tsareshi da idanu sannan ta zumbura baki takoma takwanta batareda tace masa komai ba. Abinda yaran nan zasu sakamin dashi kenan? Haba dr haidar wallahi kabani mamaki sosai yadda naga yarannan sun shigo natabbata ba asalin 6arayi bane sabida barawo bazai ta6a ajiye maka wani kudi da nufin kayi wasu bukatunka ba balle ma yaraba yabaka fiye da rabi, yadda naga fitarsu ne yatabbatarmin da akwai abinda kayi musu sukazo daukan fansa matarsa take zance yayinda ta kwantar da kanta ke rufemin baki duka duka kudinsu din nawa ne kikasani da har zakice basu saba sata ba kinsansune? Ni banason irin wannan zancen kibarni da abin dake damuna kawai. Toh Allah yabaka hakuri sukuma Allah yatona asirinsu tafada yayinda ta kuma jinginarda kanta a pilow . A6angarensu Aisha kuma khairat ce ta kula da ita alokacin da ta farka kusan azaune khairat ta kwana tausayin Aisha yacikamata rai. Allah Allah take Aisha tasamu sauki taji labarinta. Jikawai tayi tana ambaton yaya Rilwan,yaa Sagir,yaa Awwal ,baaba jummai tana ta fada tana maimaita sunan, khairat tadanyi tana sauraro bata bukatar karin bayani tasani Aisha sunakin 'yan uwanta take kira shiru tayi tana nazarin sunakin tabbas idan har tunanin datake bai raya mata karyaba wadanda suka ta6a kidnapping dinta haka sunakinsu yake, Rilwan shine wanda yatsareta kuma yake basu umarni sukebi, Sagir shine wanda yashaketa da gyalenta yajijjiga ta dashi, Awwal kuma shine wanda tasameshi akwance kamar baida lafiya awajen da suka dauketa. Tabbas haka sunakinsu yake, zuciyarta yana raya mata anya kuwa sune zai iya yiwuwa kuma yakasance basu bane , kai abin da mamaki ace kuma ansami Awwal Sagir da kuma Rilwan kuma a gida daya duk yanda akayi kidnappers dinnne, amma kuma wadancan kamar ba 'yan garin nan ba,? Koda yake garin nan da fadi yake balalle bane yakasance sune, koma dai menene idan Aisha ta samu sauki zanji ta katsae sake saken datakeyi acikin zuciyarta. Kai amma gaskiya da ace zan hadu dasu da kusan nacika buri na dan har yau inata tanadar tambayoyin da zanyi musu , hmmm daman ai na fadamusu zamu hadu kuma idan muka hadu su tanadi amsar tambayoyin dazasu sha idan kuma bahaka ba su fuskanci horo mai tsanani, hmmm inata sakar zance batareda naga su dinne ko basu bane, idan sune ma nasan zasu zo , motsin da Aisha tayi ne yakatse mata sake saken da take tayi acikin zancenta, ahankali Aisha tatashi tazauna khairat ta kuma matsowa kuda ita sannu Aisha ya jikin naki ta amsa dasauki, yawwa zaki iya tashi Aisha tace eh toh kigwada mugani Aisha ta tashi tatsaya ahankali khairat tariketa har cikin toilet suka shiga khairat tayi mata wanka sannan suka fito Aisha tahau kan gadon tazauna itama khairat zamata yi sannan Aisha ta tambayeta dazu kincemin sunan ki khairat ko? Tace eh , tace nagode sosai khairat Allah yasaka da alheri,ameeen tafada sannann tace dan Allah meyafaru dani har aka sanja min asibiti, Aisha tajefa mata tambaya sai alokacin khairat ta fahimta ashe gaskiyar doctor ne batada lafiya asali , khairat tadan saki murmushi kikwantar da hankalinki kawata babu komai zakiji komai daga baya uhm toh kuma acikin yayuna babu wanda yazo dubani? Tace eh babu wanda yazo amma su waye yayun naki ko zan san wani daga cikinsu, tace su 3 ne akwai Rilwan,akwai Awwal sannan akwai Sagir, khairat tadan zare idanu kadan sannan tace awace unguwa kuke da zama? unguwar tudu muke agidan marayu tafada cikin karfin hali. Gidan marayu kuma? Khairat tajefa mata tambaya tace eh gidan marayu amma yanzu mun bar nan munkoma gidan lauwali maishago. Khairat waye lauwali maishago kuma shifa a ina yake?, shi lauwali ai sunanshi kuma yanada shago dayake fuskantar gidan marayu. Khairat tadanyi shiru nikam dai bana fahimtar yadda kike bani amsa tafada. Alokacin wayar khairat yafara ringing tadauka taga mahaifinta ne yake mata magana misalin karfe 3 na asuba alokacin wasu masallatai sun fara kiran farko Alhajin yatambayeta ya maijikin tace jiki da sauki yanzu hakama muna hira da ita. yawwa sai godiya Alhaji yafada sannan yakuma cewa kicigaba da kulawa da ita dazaran gari yawaye zanzo. Ta ce toh sannan takashe wayar, ta dubeta malama Aisha yayunki suna sana'a ne ko suna makaranta? Eh suna yin sana'a leburanci tabata amsa tayi ajiyar zuci sannan tace toh kikwanta kiyi bacci ko? Bayan su Rilwan sun kar6o kudin daga wajen likitan sai suka zauna suka kirga naira dubu dari shida da hamsin dashi da suka lissafa awajen sannan suakyi kasafinta Rilwan yace dasafe idan Allah yakaimu zamu fita neman Aisha idan bamu sameta ba na kwanaki 2 kawai inaga kowa yakama hanyar da zai tafi, awwal yayi ajiyarr zuci yanzu ina zamuje yatambayesu , kaide ina zakaje sagir yamaida masa amsa nikam inada wajajen zuwa zantafi ko porthacourt ko lagos naje nanemi kudi acan, tunda sagir zaiyi kudu toh nikuma arewa zanyi Kano zantafi acan na tabbata zansami ayyukanyi marasa iyaka Awwal yadanyi yake hmmm nikam harga Allah har yanzu banida wajen zuwa. Toh sai ka zauna anan kayi ta fama ai sagir yabashi amsa. Washe gari da sassafe suka fita neman Aisha Haka zalika Alhaji haruna ma yaje asibiti yasami su Aisha nan khairat ta bayyana masa duk abinda suka zantar ita da Aisha daga farko har karshe alokacin har da karin bayani Aisha tayi musu sannan tasanar dasu duk abinda yafaru dasu daga farko har karshe Alhaji Haruna yace bakomai zaije yayi belin 'yan uwanta dasuke prison anjima daga nan sai ya zanta dasu.TAKE novels / HAKAN TAKE part 10 HAKAN TAKE part 10 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 16:52 Alokacin su Awwal sukaje gidan lauwali suka karya kumallon safe sannan suka sanar dashi cewa zasu je subada cikiyarta awajen jami'an tsaro sannan kuma daganan zasu biyata wajen 'yan jaridu nanma su bada cikiyarta. alokacin alhaji haruna yafita dasanyin safiya yaje offishin 'yan sanda suka bashi wajen zama bayan yazauna suna haba haba dashi dan sandan yatambaye shi yaa Alhaji yau kuma meyafaru naganka a ofishin mu. Nabiyo sawun wasu yarane ko Allah zaisa abani belinsu . Aha ya Alhaj ai kadauka kawai cewa anbaka belinsu yanzu dai su nawane kuma ya sunakinsu yake.? Alhaji ygyara zama inaji sunakinsu akwai Rilwan,Sagir,da kuma Awwal idan ban manta ba haka sunakinsu yake. Dan sanda yaja wata doguwar lumfashi sannan yace alhaji dama kanada alaka da wadancan yaran ne? Gyada kai yayi alamar eh, dansandan cikin takaici yace Alhaji mun ajiyesu har mun gaji wlh kuma kullum ko abinci babu wanda yake kawo musu haka muka gaji muka sakesu jiya jiyannan muka sakesu, Alhaji yayi ajiyar zuci sannan yace toh shikenan babu damuwa tunda kun sakesu daman nazata suna kulle ne da zanyi belinsu. alhaji yatashi zai tafi dansanda yadan riko rigarsa haba Alhaji yo akawo mana ziyara haka kawai afita batareda mun dan sami alfarma ba.? Alhaji yadanyi murmushi sannan yazaro dubu biyu yamika masa dansandan yakar6a sannan yayi godiya, Alhaji yafita, yana fita dansan yajuya yakalli dan uwansa tareda cewa sajen bukar kana gani abanza muka sake yarannan da munyi hakuri zuwa yau da munkama mai tsoka awajen Alhaji haruna, sajen bukar yadubesa ba duk kai kace asakesu ba, Alhaji haruna yatada motarsa yana tafiya alokacin su Rilwan suka iso wajen acikin adaidaita sahu suka shiga cikin ofishin 'yan sandan sajen bukar yana kallonsu yata6a dan uwansa la oga kalli ga yarannan sun kuma zuwa yadaga kai yakallesu hmmm banzaye kawai me yakawo yau kuma . Rilwan ya karisa zuwa inda suke sannan yace dafarko dai ga wannan asayi goro yamika masa dubu daya dan sandan yakarba tareda murmushi , wato munkawo muku cikiya ne nawata kanwarmu wacce ta6ata idan baka mantata ba itace ta ta6a zuwa wajenmu ranar da aka kawomu nan, eh kwarai kuwa na ganeta Allah sarki itace ta6ata dansandan yafada Rilwan yace eh dan Allah idan aka ganeta sai kukira wannan lambar wayar kusanar mana Rilwan yabashi lambobinsu duka. Dan sandan yace badamuwa insha Allahu za'a ganeta ehm sun juya zasu tafi sai kuma dan sandan yace tsaya mana dan Allah intambayeku mana, suka juyo suna jiran tambayan sagir yafada, dan Allah wane irin alakace tsakaninku da Alhaji haruna dukansu saida gabansu yafadi, wane Alhaji haruna kuma? sagir yatambaya . yace Alhaji Haruna agarin nan waye kuma baisan Alhaji haruna mai wazobiya ba. Subhanallahi dukansu suka kalli juna hmmm, meyafaru kayi mana wannan tambayan Awwal yajefama dan sandan tambaya, yanzunnan yazo nemanku nan yasamu labarin kuna prison ashe dama tunda aka rufeku nemanku yake, Rilwan yadanyi murmushi uhm ai shi bappah yake awajenmu, dan sandan yadan hada rai shine kuma baku sanar mana ba alokacin da muka kama ku? Ai da ko 30minutes bazakuyi a cell ba zaku fita. Ah kawai bamason yasani ne sabida munyiwa mai martaba rashin hankali yanzu kai kam sai anjima zamu je gidansa yanzu, yace toh madallah. Suna fita Rilwan yadubesu toh fa mahaifin khairat kuma yana nemanmu? Wannan yana nufin asirinmu yatonu yarinyar nan taganomu har ta hadamu da mahaifinta. Awwal yadubesa yanzu ba wannan ba meye abinyi? Abinyi kawai karmu kuskura mushiga hannun mahaifin khairat dan wallahi shegen attajiri ne ita kadaice fa 'yarsa sai kuma wani dansa namiji dayake karatu akasar waje, hmmm toh yanzu yabatun neman Aisha kuma. Awwal yatambaya, hmmm idan muka tsaya neman Alsha zamu iya yin biyu babu. Za'a kama mu kuma sannan zamu sha dauri mai tsanani awajen mahaifinta wanda idan mungane Aisha dinma wani tashin hankali zata sake fadawa, gaskiyarka ne. Yanzu kawai mu bar garinnan tun kafin azo akama mu dan wallahi irin wahalar damuka sha na mako biyu ma ba kadan bane balle ace ankamamu da laifin kidnapping sai ankaimu kotu fa sannan za'a yanke mana hukunci nikam wallahi bazan zauna ba. Suka tashi kai tsaye sai tasha ko lauwali basu sanarwa ba suka kama hanya kawai daga birnin yola sai a jalingo aka saukesu atasha suka fito kowannensu da jaka ahannunsa sannan suka tare wani dan adaidaita suka tambayesa ko akwai wani hotel anan garin, yace eh kwarai akwai camp lavet hotel Rilwan yace toh kaimu can haka mai adaidaita yakaisu sannan yasaukesu suka shiga ciki suka kama hayan daki , ehen sai yanzu hankalina yakwanta domin inaga mun tsira yanzu kam, aha yawwa yabatun watsewan dazamuyi din Rilwan yatambaya hmm nidama na fada maka lagos zan tafi ko porthacourt uhm toh kaikuma fa Awwal har yanzu baka fada ba Rilwan yajefa masa tambaya Awwal yace kai nifa har yanzu tunawa nakeyi yanzu kai idan kaje kano me zakayi acan, Rilwan ya tuntsire da dariya haba yaro kaifa kawai kallona kake ai idan naje kanon nan wallah nema zanyi kamar ba gobe, yakamata kaima kasami wani babban gari inda zaka samu kudi koda bakada jari sagir yafada, uhm toh ya ko zakaje Maiduguri ne? Kutt bakada Hankali wa nidin kake kirawa maiduguri? Rilwan harda kyalkyala yake meyasa bazakaje maiduguri ba yatambayi awwal. Wai yama zan fara tashi daga Adamawa kuma inkoma maiduguri ne? Wallahi gara nakoma baban khairat yadaureni kawai, toh yanzu abinda za'ayi tunda bakada wajen zuwa sai mutafi tare ko ya ka gani? Ok toh nine Saniyar ware kenan nima sai dai mutafi tare, idan muka tafi tare kuma ai anyi ba'ayi ba saidai idan mukaje kowa yanemi sana'ar da zaiyi. Yawwa yanzu naji magana toh yanzu ina zamu wuce daga nan, inaga mudan zauna kwanaki 2 mugani idan ana samu anan da sai mu zauna basai munyi dogon tafiya ba awwal yafada. Kuma hakane fa suka ajiye shawara akan zasu zauna. Adayan 6angaren kuma Alhaji Haruna yakoma yasami Aisha yasanar mata cewa an sakesu sai dai yanzu baisan inda suke ba, yaje gidan marayunma yaga ba yanda yasaba ganinta take ba babu alaman mutane aciki sabida ana gyara har yanzu, Aisha tayi ajiyar zuci sannan tace toh inaga bazasu wuce wajen lauwali mai shago ba. suka duru cikin mota da khairat da mahaifinta dakuma Aisha basu tsaya ko ina ba sai kofar shagon lauwali. Yana ganinta cike da mamaki Aisha ina kika shiga kwana 2 muna ta nemanki har ansake yayunki suma yanzu haka suna can sunata nemanki , Alhaji Haruna yakwashe labarin duk abinda yafaru yasanar ma lauwali sannan yace abashi lambar wayansu idan yaso ace musu sudawo gida lauwali yace baida lambarsu amma sunce masa zasuje station subada sanarwa sannan kuma zasu je wajen 'yan jarida inada tabbacin idan sukaje zasu bada lambobin wayarsu. Hakane tabbas zasu bada yanzu bari mukoma station din tukunna suka kama hanya sai police station suka shiga kai tsaye dan sandan yace yawwa Alhaji yaranka kana tafiya suka zo sunkawo cikiyar kanwarsu, ha'a Alhaji yafada yayinda abin yafara 6ata masa rai, yanzu ina suke ? Tunda safe nake maka zance harma lambobin wayansu suka bayar idan ansameta akirasu. alhaji yace gatanan ai yanzu bani lambar su din nakira, Suna kwance cikin daki wayar Rilwan tafara kadawa. Dasauri yaduba yaga bakon number sannan yadauka yakara ta akunnensa tareda yin Sallama wa alaikassalam kana magana da Alhaji Haruna mai wazobiya yafada Rilwan yaji hanjin cikinsa ta kada nan take ya katse kiran sagir yadubesa lafiya yace mahaifin khairat ne yakirani yanzu kawai ya kashe wayar sannan ya wurgar da ita agefe. Alhaji yace ha'a yakuma yakashe wayar . alhaji yasake kira sai yaji wayar akashe , sai yadubi dan sandan yace bani lambar sauran. Suna kwance wayar Awwal ma tafara ringing yaduba sai yaga bakon lamba shima sai yakara akunnensa tareda sallama nanma sai yaji ance Alhaji haruna ne ya akayi muna waya da dan uwanka yakatse kiran sannan kuma yakashe wayarsa? Awwal shima bai tsaya nan ba kawai yakatse kiran sannan yakashe wayar , Sagir yana ganin haka kawai shima sai ya kashe wayarsa tun kafin akirashi, Alhaji Haruna yayita gwadawa abin yaki. Har yagaji yahakura khairat gabadaya ta fahimci al'amarin wato sun fahimci cewa mahaifina yana nemansu azatonsu nasanar dashi labarinsu ko? Hmmm tadubi mahaifinta Abba abani lambarsu zangwada kira anjima. Ko musu baiyiba yabata lambobinsu duka. Tayi saving dinsu. Sannnan lauwali yakama yima Alhaji haruna godiya Alhaji yace babu komai idan sun dawo kace musu ina nemansu Lauwali ya amsa toh sannan yace Aisha yanzu sai mutafiko? Khairat tace a'a malam lauwal kayi hakuri kakyale Aisha ta zauna taredamu dan Allah, lauwali yace a'a gaskiya shi baida ikon wannan amma idan ita Aishan zata iya zama daku kuma tana so nikam babu wata damuwa awajena, khairat tadubeta Aisha zamu zauna tare ko? Aisha ta danyi murmushi sannan tace eh zamu zauna amma kullum zan rika zuwa wajen Fatima da Bilal agidan lauwali, Alhaji dai baice musu komai ba har suka gama sasantawa shidai yashiga sassarfa wane dalili ne yasa yaran nan suketa kauce masa haka, yaka sa gano amsar tambayan. Washe gari da safe gari ya gama wayewa su Awwal suka fita kowa yakama hanyarsa, Har misalin karfe 12 na rana kowannensu bai samu aikinda yakamaba. Rilwan yagaji dayawo shikadai yasami wani bishiya yazauna yana tunani kai gaskiya neman halal da wuya yake, yanzu da haram zan nema da tuntuni nasamu yana cikin tunanin sai yahango wani shagon aski gayu ne kawai aciki sunata shewa suna surutu sai kawai yatashi yaje shagon danufin aske gashin kansa sabida alokacin kanshi yahada suma, yashiga yazauna yayi shiru yana tunani ko angane fatima yanzu Allah ne masani. agefensa yahango wani gaye yanata faman danne danne da waya ahannunsa Sannan kuma yaga yadaga wayar yakara ta akunnensa yafara magana cikin disar da murya bisa dukkan alamu yanaso ne yayi irin magana cikin muryar mata amma abin yagagara sai yasaka kiran on hold yajuya yakalli abokansa dake wajen dan Allah anan waye zai iya magana da muryan mata wani gaye agefe yafara magana sai kuma yakasa duka suka gwada abin yaki. Daga nesa yahango Rilwan sai yaga yanata kallonsa sabida haka sai kawai yayi masa signal alamun yazo Rilwan yakaraso inda yake sannan yace yi magana muji nanfa Rilwan yatsuke murya yayi kadan gayen yace goood karbi wannan wayan zakayi magana da kawuna yafada masa duk abinda zaice masa sannan yamika ma Rilwan wayar ahankali Rilwan yakar6a yakara akunnensa yafara da cewa i am sorry for holding your call mysweat, yace ba matsala Babyna ke ai tawace idan ban 6ata lokacina danke ba danwa zan 6ata. nanfa suka fara zance kota ina mutumin yafito sai Rilwan ya tarosa tanan haka Rilwan yagama masa zance sannan yace zan turo miki kudin ta Numbern account din da kika bani a whatsApp. Yace shikenan nagode sokayi bankwana, sannan yakashe wayar , Rilwan yana gamawa wancan gayen yayi tsalle sannan yasauka sabida murna yamikawa Rilwan hannu suka tafa sannan yace ur brain is logic ya sunanka? yace sunana Rilwan good Rilwan me sana'arka? Rilwan yace babu sai gayen yace great kai abokin tafiya ne, Ni kuma sunana Sadauki. A ina kakeda zama Rilwan yace a Camp Lavet Hotel Jalingo 11Aganwa street yace ok good kai bakone agarin nan ko? Rilwan yace eh sannan gayen yace bani lambar wayanka Rilwan yabashi akwai wani ma agefe yana zaune yace nima bani lambarka Rilwan yaraba musu lambarsa sannan gayen yazaro kudi Naira dubu biyar sabbi yamika masa yace gashi wannan kadan yi manage kafin mu hadu gobe. Yace toh bakomai. Akayiwa Rilwan aski yatashi zai tafi gayen yakirasa yazo sannan yace i hope you are goood in social networks and you have a littile knowledge of operating the computer.? Rilwan yadanyi yake eh toh nadanyi facebook sannan kuma nata6a 2go sai dai bandade inayi ba nasayar da wayar tundaga lokacin nadena hawa. Sannan computer kuma alokacin da muke makaranta muna dan kokari domin kuwa acikin ajinmu mune muke kokartawa a computer studies. sadauki yace toh ba komai naji dadin haduwa dakai idan baka iya bama zan koya ma sabida kai abokin tafiya ne. TAKE part 11 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 16:54 Rilwan yakama hanya bai tsaya ko ina ba sai mazauninsu yana zuwa yasami Sagir yana kwance adaki. Yashigo ya toh bross meke going ne Rilwan yatambaya yana dan bouncing cikin yanayin fara'a. Hmmm kabari kawai nawa wallahi neman halal da wuya yake, tun dana fita yawo nake naje wani waje abakin tasha nasami wata mota takawo kaya wasu guys suna saukewa kawai nima saina shiga nakama yi saida muka gama naje nace asallameni sannan sukace wai waye ya gayyaceni? Rilwan ya kyalkyale da dariya kana nufin basu baka ko sisi ba kenan? Ah sun bani amma da kyar nasami naira dari biyu da hamsin shi dinma nashiga wani restaurant naci abinci saida nayi ciko. Rilwan yazauna yayi dariya sannan yace ai abu yayi daman ana nemane saboda aci tunda kasamu kaci saika godewa Allah , Sagir yace hakane kam Allah shine abin godiya. ka bari kawai dukwanda kaga yana neman halal dinsa ko wane irin sana'a yakeyi wallahi bakaramin mai tawakkali bane awannan zamanin. Gaskiya kam abin akwai wahala ya kaifa mekanemo mana. Rilwan yadanyi murmushi sannan yace ai inaga gwara kaima kasami kayi wani aiki amma ni wallahi haka nakarashi yawona babu abinda nasamu amma dayake Allah ya kaddara ni mai rabone nahadu da wani smart guy kagansa yanda ya hadu kuwa? Sunansa Sadauki haka yacemin Wallahi irin gayu shahararrun nan ne ba irin wadanda dakyar ake sayan kaya sai kuri ba, shi wancan aiki kadan nayi masa zance da baki yadauki dubu biyar yabani, sagir cikin mamaki dubu biyar wanne irin magana kayi haka wanda har zai dauki dubu biyar yabaka? Rilwan yadanyi murmushi sannan yakwashe bayani kaf yasanarma Sagir. Suna cikin haka sai ga Awwal yashigo shima yana dan murmushi ya mekasamo mana ne? Yace ai ku bari kawai guys garin nan akwai wahala musamman yunwa atake yake galabaitar da mutum, tunda nafita naketa yawo babu abinda nasamu Allah yataimaka inada kudi dashi nayi amfani nasayi abinci. Aranar lauwali mai shago da Aisha sukayi jiran dawowansu Rilwan har suka gaji amma basu dawo ba har dare Aisha da khairat suka koma gida danufin gobe da safe zasuyi sammako suje gidan lauwali ko zasu samesu agida. Haka suka wuni har yamma basy dawo ba nanfa suka shirya suka koma gida. Bayan sunje gida sun kwanta adakin khairat sai khairat take tambayar Aisha cewa: natambayeki kuma kin bani amsa amma ina mai shakkar amsar dakika bani Aisha tadanyi sannan tadubi khairat menene tambayar ? Me sana'ar yayunki kikace min leburanci toh amma gaskiya nifa ban yadda ba, Aisha tadubeta cikin alaman tambaya meyasa baki yadda ba khairat zanyi miki karyane? Khairat tadanyi ajiyar zuci sannan tace Aisha bahaka nake nufi ba abinda nake nufi shin tunda kike kinta6a tunanin cewa yayunki suna aikata kidnapping? Wani dumm Aisha taji wani abu a zuciyarta mamaki yacika zuciyarta tabbas akwai lokacin da Rilwan yake fadamata cewa ke 'yar uwarmu ce sabida haka bazamu 6oye miki komai ba Aisha muna aikata kidnapping tayi wannan sakar acikin zuciyarta, sannnan tadubi khairat meyasa kikayimin wannan tambayar, Khairat tadanyi murumushi sabida sunta6a yin kidnapping dina kuma sun kar6i kudi Naira dubu dari biyu, alokacin wasu hawaye masu radadi suka fara kwaranya daga idanun Aisha yayinda tataso ta dafa khairat sannan tace kiyi hakuri yayuna sun ta6ayin kidnapping tun alokacin muna gidan marayu babu abinda zamu ci shiyasa suka je suka aikata wannan aikin kuma bana tunanin sun kara yin wani bayan wancan Aisha ta kwashe zancen duka ta labartawa khairat. Madallah nagodewa Allah yanzu nasami amsoshin tambayoyin dana ke ta faman kwana da tunani akansu. Tabbbas zan iya goyon bayan hakan sabida wasu alamominsu yasha bamban dana sauran kidnnapers , yanzu dai zan kira lambarsu sannan nace musu su zo kina wajena . Eh toh kina ganin zasu zo kenan? Uhm bari dai mubari sai gobe zuwa yanma idan basu zo nemanki ba sai mukirasu awaya ko? Suna cikin hirar sai wayar Sagir tafara Ringing yaduba sai yaga bakon lamba. Yadaga kai ahankali yakalli 'yan uwansa , Rilwan yace ina fatan ba lambar Alhaji haruna bane? Eh tabbas wannan ba tashi bace . Sagir yadauka sannan yakara akunnensa yayi sallama sai yaji muryar mace , sabida haka sai yasaka wayar a free hands yadda 'yan uwansa zasu ji zancen wanda yake magana dashi, da waye nake magana sagir yatambaya ? Kana magana ne da 'yar kidnapping .. 'yar kidnapping kuma wacece kuma 'yar kidnapping, hmmm kana so kacemin kamanta da khairat. Nanfa ya kwashe da dariya malama khairat wato kin sanarwa mahaifinki cewa mune mukayi kidnapping dinki bayan kinyi bincike kingane mazauninmu ko? Haba kai kuwa da ace inada niyyar kamaku da ko kwana 1 bazakuyi ba za'a kamaku amma sabida ina tausaya muku shiyasa na saukake muku wahala, toh naji shikenan malama khairat kin kyalemu yanzu menene dalilin dayasa kika kirani awaya shin wai kinsan ko da waye kike magana ma kuwa? Tace nasani mana bakaine Rilwan ba? A'a bani bane Ni sagir ne, au kacemin da mugun cikin nake zance, Yadanyi murmushi suko Rilwan da Awwal sun kasa kunnuwa suna sauraron tadin dake gudana tsakanin Sagir da kuma Khairat. Yanzu menene dalilin kirana da kikayi. Yawwa nagode daka tambayeni tin kafin nasanar dakai, da farko dai ina nemanku inaso mutattauna daku. Ke dakata bana son shirme dan Allah karki maidamu dakikai mana , kinzata bamu da labari mahaifinki yana neman mu ne? Abinda nakeso nafada miki shine kawai kijanye daga kudirinki na kamamu dakikeyi dan bazaki ta6a cin nasara ba. Idan kuma kikayi wasa sai mun sake saceki tukunna. Hhhhhh kawai ta kwashe da dariya a ina kata6a jin anyi kidnapping na dan kidnapping ai idan baka sani ba nima yanzu 'yar kidnapping ce, nasani kanwarku ta6ata kuma kuna nemanta , bakowabane ya saceta illa ni dan yanzu haka tana wajena . Idan kuna so ku karbi kanwarku dole ne ku zo har gidanmu sannnan kuma yakasance kunzo akan lokaci. A'a khairat kinga wallah Karkiyiwa Aisha komi sai tasaka hannu tariko khairat sannan ta kashe mata idan Aisha sai ta saki ihu wayyoo yayaaaa dan Allah kutaimakeni kuzo. Rilwan dake zaune ji yayi kawai yatashi yatsaya wato ita wannnan yarinyar game din da shirya mana kenan. Yace ma sagir bani wayar. Yamika masa Rilwan yakarba ransa a6ace ke khairat me kike nufi damu ne? Yawwa yanzu nakejin zance tafada sannan tace Rilwan ko? Nasan basai na maimaita maka abinda nafadama dan uwanka ba. Kawai kuzo ku kar6i kanwarku ni bansanarwa Abbana komai ba. Rilwan yadanyi ajiyar zuci sannan yace toh yanzu haka mudai bama gari. Sabida haka kome zakiyi mata sai kiyi wannan ba damuwar mu bane. Sannan yakashe wayar Awwal yatashi kai Rilwan kasan me kace kuwa? Ko me zatayima Aisha tayi fa kafada. Eh kwarai kuwa. Sagir yace toh me dalilinka na fadan hakan. Hmm sabida nasani bazata yiwa Aisha komai ba. Kana magana sai kace bakasan ya kidnapping yake ba. Da ace wasu manyan 'yan kidnap ne zan iya tuna cewa zasu iya yimata wani abu ko kuma su kasheta amma khairat natabbata plan kawai take hada mana kaga idan ma takamata ne dan kidnap yanzu haka saketa zatayi sabida koda tariketa matukar tasani bazata sami biyan bukatantaba tuni zata saketa. Ai muma alokacin can da ace mahaifin khairat yace mudauki duk hukuncin damuka ga zamu iya akan 'yarsa da saketa zamuyi ta tafi amma ya kagani daya nuna yadamu sai da muka cajeshi kafin muka saketa. Eh kwarai kuwa hakane zancen nan naka. Khairat tayi wurgi da wayarta tsabar haushi Rilwan din nan yagano lagonta yanxu ko? Hmm sai tadubo Aisha sannan tace anjima zan kirashi sai kuyi magana tare ko? Aisha tamasa toh shikenan. Ana kwana ana tashi abota sai kara kargo yake tsakanin Aisha da khairat suko su Rilwan sun shareta sunyi irin ko inkula akullum Aisha saitaje gidan lauwali maishago takaiwa kannenta tsaraba. Abangarensu Rilwan kuma washe gari da misalin karfe tara yana kwance adaki saiga kiran wayan sadauki yashigo masa dasauri yakama sannan ya gaishesa sai Sadauki yace masa yanzu haka yana kofar camp lovet hotel yasabida haka yafita sutafi yana sauri. Cikin Hanzari Rilwan yatashi yasanarwa su Awwal zaije yanzu Sadauki yakirasa. Yashirya yafita yakalli wata mota corolla ta tsaye abakin kofa, kai tsaye yaje yasameshi sannan yamika masa hannu sukayi musabaha daga bisani suka shiga mota suka tafi. Awani gida mai kyau suka faka sannan suka fito daga motar Sadauki yace zo mushiga ciki kaitsaye kawai suka wuce har cikin wani palo wasu gayi suka samu su 2 suna buga tv game ps3 Rilwan yazauna akan kujerar yanata kalle kallen gidan kai gaskiya gidannan yayi bakarya dubi yadda wadannan gayun suke more rayuwansu anan. sadauki kai tsaye yawuce cikin daki sannan yafito da computer ahannunsa yakawo ma Rilwan sannan yakunna yadubesa abokina ka iya sarrafa hoto a computer . Rilwan yagyada kai tareda cewa eh toh ina dai kokari. Toh gashi inaso kassarrafa min wannan hoton ta yadda yadda zai kayatar sosai . Rilwan yakarbi computer din sannan yadubesa ina bukatar internet connection yafada masa. sadauki yaciro modem a cikin alhjihunsa sannan yamikama Rilwan yakar6a yasaka Sai Saidauki yace ina ciki iidan kagama Sadauki yawuce daki. Rilwan yana hawa ne yaje yasaukarda photo shop. Sannnan yagyara hoton mai kyau, sadauki yana zuwa yagani yace goood abin yayi kyau wlh . Aha Rilwan yace mai gida kenan ina da tambaya Sadauki yace toh ina jinka. Rilwan yace menene Sunan Sana'ar ka wanda nake shirin shiga yazo. sadauki yayo dariya sannan yace karka damu abokina zan fada maka amma mu a6oye muke. Shin Ko kasan wandanda ake kira yahoo boys a shafukan yanar gizo? Dasauri yatashi yatsaya daga zaman da yake yahooo boys? Bisa dukkan alamu jin sunan yahoo boys yadaga masa hankali, sabida yadda yafara hada gumi awajen duk da air condition din dake zubar da ra6a aduk sassan dakin. Budan bakinsa sai yace Hakan take.KE novels / HAKAN TAKE part 12 HAKAN TAKE part 12 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 16:56 Bisa dukkan alamu jin sunan yahoo boys yadaga masa hankali, sabida yadda yafara hada gumi awajen duk da air condition din dake zubar da ra6a aduk sassan dakin. Budan bakinsa sai yace amma maigida yahoo boys dinnan 'yan fasa kwauri fa kenan? Sadauki yadanyi murmushi kwantar da hankalinka samrt guy hakane 'yan fasa kwauri kamar yadda kafada karka damu idan kana taredamu zaka samu kudi sannan kuma kullum zaka rika kara ilimi zaka zamto daban ne acikin jama'a sannan mutane dayawa zasu kasance masu sha'awa da duk wasu actions dinka all we need is just your confidence, Rilwan yadanyi shiru sannan yace shin yanzu taya za'ayi nafara wannan aikin? Sadauki yace karka damu kaga yadda kayi magana da wancan mutumin dana baka wayata? Haka zaka kasance kana sarrafa tunaninka sannan yakasance kazama mai nacewa dashiga shafukan yanar gizo. Akwai bukatar kasan yaruka na sarrafa computer (programming languages) wadanda keda matukar wahala amma idan kwakwalwarka tana da nitsuwa zaka fahimcesu ahankali. Sannan kuma zaka nemi ilimin kutse acikin shafukan yanar gizo (hacking) domin samo bayanai masu muhimmanci. Rilwan yadanyi ajiyar zuci sannan yadubesa, toh wannan shine ake kira kutsen kam amma babu komai zan jarraba sai dai ayanzu haka banida waya wanda zan iya shiga yanar gizo da ita, ok karka damu Sadauki yafada sannan yace katuna min ma daukomin wancan jakar akwai wayoyi acikinta . Rilwan yatashi ahankali sannan yaje yadauka yakawo sadauki yace bude kagani yana budewa yakalli wayoyi sabbi aciki tafarko akwai java phone nokia c3 sai kuma symbian nokia E6 sai kuma Android techno c8 da Black-Berry bold 9790 da kuma iphone sannan yace inaso yakasance ka kware wajen amfani da dukkan wadannan wayoyin sannan kuma computer zaka lallaba da nawa sai muke yin amfani dasu duka kafin kasamu kamallaki taka takanka. Rilwan yace nagode sosai toh amma wadannan amfani dasu ai kudin simcard ma da kuma subscription dinsu ma ai ya ishe mutum kashe kudi, sadauki yatuntsire da dariya yayin da Rilwan shi ko ajikinsa gani yake kawai shi yanzu ta waru masa, sadauki yace karkadamu zaka na amfani ne da wifi idan za'a yi aiki sosai idan kuma bawani aiki sosai bane da modem zakayi aiki subscription karka damu mu koba data muna hawa net because munsan duk wata hanyar shiga yanar gizo ta bayan fage. Rilwan yadanyi murmushi sannan Sadauki yace dauki c3 dinnan kasaka simcard dinka ka ajiye taka wayar baby nokia incase sabida itama tana da amfani nangaba , Rilwan yadauka yakunna sannan sadauki yace kanada data din dazaka iya shiga Rilwan yace a'a sadauki yadauko ipad dinsa yadannawasu lambobi sai gashi 2g.5b sun shigo wayar sa sannan Sadauki yace yanzu zaka iya shiga. Kadaura duk wasu abubuwan dakake amfani dasu akai sannan kafara chatting da friends dinka na 2go kayi 30minutes kanayi, sannan kashiga Room go trivia kayi 15 minutes sannan kuma kashiga go words nanma kayi 15 minutes idan kahada kaga kenan kayi 1 hour. Natabbata zakajika action dinka yadawo sannan kuma experience dinka zasu dan fara daga nan kuma sai ka sauka karufe 2go din kahau facebook idan kahau inaso kayi wani posting wanda zai kayatar atakaice inaso naga anyi comment atleast 10 acikin 3 hours. Bayan nan kuma sai kaduba chats dinka s kadanyi hira da friends dinka shima na 20 minutes sai kuma kabibiyi news feed nanma ka dauki kamar 20 minutes kanayi sannan kuma kayi searching na hackers dakuma webmasters yazamana akwaisu acikin friends dinka , yakasance duk wani link dinda suka turo zakabi. (hackers sune masu kutse acikin yanar gizo webmaster kuma sune masu zana shafukan yanargizo link kuma yana nufin rariyar likau na shafin yanar gizo) amma karka shiga whatsAp tukunna, idan kagama sai kayimin magana ni ina ciki sadauki yawuce kai tsaye cikin daki . Rilwan yahau direct yadauko 2go sannan yasaukar dakukar da uc browser da kuma whatsapp jar sannan kuma yasaukar da facebook. Nanfa yahau aiki kamar yadda sadauki yafadamasa shine bai gama ba sai bayan 4hour sannan yagama yaje yasami sadauki yasanar masa yagama sai sadauki yace toh kabude whatsap ma kayi 15 minutes idan kagama sai ka kashe wayar kacire simcard din sannan kasakata acikin waya symbian dincan itama kasaukarda duk apps din dana gayama saikashiga kagani. Rilwan haka yayi bayan yagama sannan yakuma sanar da sadauki yagama wannan kam acikin 2hours yayi, sannan sadauki yace very goood yanzu iinafatan zaka iya bambance dadin java phone dakuma symbian Rilwan yace eh kwarai kuwa zan iya toh menene bambancin Rilwan yadany ajiyar zuci sannan yace dafarko java phone batada sauri kamar symbian, sannan kuma symbian tana daukan application na java wato ,jar da kuma nata ita kuma java na java kadai take budewa. Sannan kuma symbian app agaban sunansu .sis ne ko .sisx shikuma java .jar ko kuma .jad sannan kuma symbian tana minimize ita kuma java batayi. Sadauki yayi murmushi sannan yace you are Really smart brain da ka shiga whatsAp na symbian da kuma najava bakaga banbanci ba? Eh tabbas naga banbanci sabida akwai wasu abubuwa wadanda ajava bana kallonsu misali kamar su smileys idan ina rubutu babu daman ina amfani dasu yadda nakeso amma a symbian ina amfani dasu yanda nakeso . Sannna kuma symbian tana da saurin bude message fiyeda java . (smileys wasu alamomi ne wadanda ake amfani dasu a whatsAp ko wasu safukan sada zumunat musamman wajen nuna shauki dakuma aikatau) Sadauki yace good yanzu abinda nakeso kayi next kacire simcard din again kasaka acikin black Berry dinncan idan kagama sai kasakata a cikin android bayan kagama sai kasakata acikin iphone idan kagama sai kazo kasanardani bambancin dake tsakaninsu gaba daya haka Rilwan yayisu daya bayan daya shine baigamaba sai da aka kusan kiran sallar magariba sannan yagama, yasanarwa Sadauki sanann yayi masa tambayoyi gabadaya ya amsa masau tamkar yadda yayi na wadancan, dakyau sadauki yafada sannan yace yanzu zamu dakata anan sabida haka inaso kaza6i wayar da zaka tafida ita yau kaleka friends dinka kuyi chatting dasu. Rilwan yadauki Symbian e6 din sannan yace zance nayi da wannan sabida ina marmarin wayar Sadauki yace ok toh badamuwa sadauki yaciro dubu 7 yabashi Rilwan yakar6a tareda godiya sannan yafita yakama hanyar gida yana fita yatare dan aca6a yakaisa hotel din dasuka sauka sannan yaciro Naira dari biyu yamikawa dan aca6an yajuya zai tafi dan aca6an yace abokina kamanta canjinka Rilwan yadan juyo tareda cewa nawane canjin naira dari da hamsin ne canjinka. rike nabarmaka kawai. dan aca6an yayi godiya Rilwan oh yau kuma nine da kyautar kudi har naira dari Da hamsin? Allah mai iko .yashiga kai tsaye yasami su Sagir suna zaune suna cin balangu acikin daki. Yana shigowa yace kuut yau ta waru kenan ? Har da nama kukaa saya mana ? Kai amma wallahi shine nake gayamaka mucinye naman nan tunda wuri ka shareni kuma kasan Rilwan mayen nama ne kamar kura Sagir yafada cikin wasa . Hmmm toh dan kaniyarka sai naci Rilwan yafada yayinda yazo yacika hannin sannan ya harba cikin bakinsa yana taunawa awwal yace kai dan banza zaka kware fa wallahi. Ah to in kware din mana Rilwan yafada yayinda yazauna yaciro wayarsa E6 yafara dannawa uhm kasayi waya ne? awwal yatambayeshi uhm oga nane yabani duk acikin training ne Rilwan yabashi amsa yayinda yamaida hankalinsa akan waya sagir kuma yana cin nama.. Dakyau yafada sannan yace baka tambayemu ba kazo kasamemu muna cin nama? Ehen yawwa daman ina da niyyar yimuku wannan tambayar. Wata hajiyace kawai tana wucewa tazo sayan nama awajen wannan mai saida balangu abakin titin nan taganmu muna zaune tace yabamu na dubu 1 kut. Ah lalle kuwa kun cikaro da mata mai sakin hannu amma kunyi mata godiya kuwa? Kuut kwarai kuwa munyi mata godiya harma takar6i lambar wayan Sagir. Taaab kace zaku zama mazajen hotiho mana? Rilwan yafada cikin nishadi Kai suwaye mazajen hotiho zan mazgeka wallahi Sagir yadaka masa harara. Alokacin wayar Awwal tafara ringing ahankali yadauka sannan yace Hello wake magana? khairat ce aka bashi amsa yadan nitso kadan sannan yace khairat kina lafiya tace lafiya lau nasan bakada zancen dazakayimin nakira ka ne sabida kanwarku tanason yin magana da ku sabida haka gatanan kuyi magana, Aisha ta kar6i wayar zancen farko kuka kunnen Awwal suka fara jiyo masa sannan ne yace Aisha meyasameki Aisha me khairat tayi miki? Babu abinda khairat tayimin Sai alheri, tunda ku yafldani kukayi, ina yaya Rilwan da sagir? Suna kusa dani yawwa toh kasaka wayar afree hand yanda zan iya yin magana daku duka kowa yafada awwal yace toh sannan yasaka waya a free hands. Muna sauraronki yafada sai tafara dacewa amma yayuna kun bani mamaki , ashe zaku iya banzatar dani , ashe zaku iya nunamin cewa kowa ye iyayensa daban atsakaninmu? Ashe zaku iya nuna min cewa koda za'a kasheni babu ruwanku? Meyasa kuka 6uya kuka ki zuwa koda kudubani ko dan kukalli wane irin hali nake ciki? Yau kwana ki 3 kenan da aka sakeku daga gidan yari amma sai gashi kunkasa neman inda nake kodan kuji me nake ciki? Nasani kunsami labari kannenmu sun rasu fatima da Bilal ne kadai suka rage sai ni, dakukaje kuka gansu shikenan nikuma baku damu da ku ganni ba ko? Dukkkan jikinsu yayi sanyi Sabida bayanin da take ta zubo musu, Rilwan yace kiyi hakuri Aisha wallahi.闂傚倸鍊搁崐鎼佸磹閹间礁纾归柟闂寸绾惧綊鏌熼梻瀵割槮缁炬儳缍婇弻鐔兼⒒鐎靛壊妲紒鐐劤缂嶅﹪寮婚悢鍏尖拻閻庨潧澹婂Σ顔剧磼閻愵剙鍔ょ紓宥咃躬瀵鎮㈤崗灏栨嫽闁诲酣娼ф竟濠偽i鍓х<闁绘劦鍓欓崝銈囩磽瀹ュ拑韬€殿喖顭烽幃銏ゅ礂鐏忔牗瀚介梺璇查叄濞佳勭珶婵犲伣锝夘敊閸撗咃紲闂佺粯鍔﹂崜娆撳礉閵堝洨纾界€广儱鎷戦煬顒傗偓娈垮枛椤兘骞冮姀銈呯閻忓繑鐗楃€氫粙姊虹拠鏌ュ弰婵炰匠鍕彾濠电姴浼i敐澶樻晩闁告挆鍜冪床闂備胶绮崝锕傚礈濞嗘挸绀夐柕鍫濇川绾剧晫鈧箍鍎遍幏鎴︾叕椤掑倵鍋撳▓鍨灈妞ゎ厾鍏橀獮鍐閵堝懐顦ч柣蹇撶箲閻楁鈧矮绮欏铏规嫚閺屻儱寮板┑鐐板尃閸曨厾褰炬繝鐢靛Т娴硷綁鏁愭径妯绘櫓闂佸憡鎸嗛崪鍐簥闂傚倷鑳剁划顖炲礉閿曞倸绀堟繛鍡樻尭缁€澶愭煏閸繃宸濈痪鍓ф櫕閳ь剙绠嶉崕閬嶅箯閹达妇鍙曟い鎺戝€甸崑鎾斥枔閸喗鐏堝銈庡幘閸忔﹢鐛崘顔碱潊闁靛牆鎳愰ˇ褔鏌h箛鎾剁闁绘顨堥埀顒佺煯缁瑥顫忛搹瑙勫珰闁哄被鍎卞鏉库攽閻愭澘灏冮柛鏇ㄥ幘瑜扮偓绻濋悽闈浶㈠ù纭风秮閺佹劖寰勫Ο缁樻珦闂備礁鎲¢幐鍡涘椽閸愵亜绨ラ梻鍌氬€烽懗鍓佸垝椤栫偛绀夐柨鏇炲€哥粈鍫熺箾閸℃ɑ灏紒鈧径鎰厪闁割偅绻冨婵堢棯閸撗勬珪闁逞屽墮缁犲秹宕曢柆宥呯闁硅揪濡囬崣鏇熴亜閹烘垵鈧敻宕戦幘鏂ユ灁闁割煈鍠楅悘鍫濐渻閵堝骸骞橀柛蹇旓耿閻涱噣宕橀纰辨綂闂侀潧鐗嗛幊鎰八囪閺岋綀绠涢幘鍓侇唹闂佺粯顨嗛〃鍫ュ焵椤掍胶鐓紒顔界懃椤繘鎼圭憴鍕彴闂佸搫琚崕鍗烆嚕閺夊簱鏀介柣鎰緲鐏忓啴鏌涢弴銊ュ箻鐟滄壆鍋撶换婵嬫偨闂堟刀銏犆圭涵椋庣М闁轰焦鍔栧鍕熺紒妯荤彟闂傚倷绀侀幉锟犲箰閸℃稑妞介柛鎰典簻缁ㄣ儵姊婚崒姘偓鐑芥嚄閸撲礁鍨濇い鏍仜缁€澶愭煥閺囩偛鈧摜绮堥崼鐔虹闁糕剝蓱鐏忣厾绱掗埀顒佸緞閹邦厾鍘梺鍓插亝缁诲啫顔忓┑鍫㈡/闁告挆鍕彧闂侀€炲苯澧紒鐘茬Ч瀹曟洟鏌嗗鍛唵闂佺鎻俊鍥矗閺囩喆浜滈柟鐑樺灥閳ь剛鏁诲畷鎴﹀箻閺傘儲鐏侀梺鍓茬厛閸犳鎮橀崼婵愭富闁靛牆楠搁獮姗€鏌涜箛鏃撹€块柣娑卞櫍瀹曟﹢顢欑喊杈ㄧ秱闂備線娼ч悧鍡涘箠閹板叓鍥樄闁哄矉缍€缁犳盯骞橀崜渚囧敼闂備胶绮〃鍡涖€冮崼銉ョ劦妞ゆ帊鑳堕悡顖滅磼椤旂晫鎳冩い顐㈢箻閹煎湱鎲撮崟顐ゅ酱闂備礁鎼悮顐﹀磿閸楃儐鍤曢柡澶婄氨閺€浠嬫煟閹邦厽绶查悘蹇撳暣閺屾盯寮撮妸銉ョ閻熸粍澹嗛崑鎾舵崲濠靛鍋ㄩ梻鍫熷垁閵忕妴鍦兜妞嬪海袦闂佽桨鐒﹂崝鏍ь嚗閸曨倠鐔虹磼濡崵褰熼梻鍌氬€风粈渚€骞夐敓鐘茬闁糕剝绋戝浠嬫煕閹板吀绨荤紒銊e劦濮婂宕掑顑藉亾閻戣姤鍤勯柛鎾茬閸ㄦ繃銇勯弽顐粶缂佲偓婢舵劖鐓ラ柡鍥╁仜閳ь剙鎽滅划鍫ュ醇閻旇櫣顔曢梺绯曞墲钃遍悘蹇e幘缁辨帡鍩€椤掍礁绶為柟閭﹀幘閸橆亪姊洪崜鎻掍簼缂佽鍟蹇撯攽閸垺锛忛梺鍛婃寙閸曨剛褰ч梻渚€鈧偛鑻晶顔剧磼閻樿尙效鐎规洘娲熼弻鍡楊吋閸涱垼鍞甸梻浣侯攰閹活亝淇婇崶顒€鐭楅柡鍥╁枂娴滄粓鏌熼悜妯虹仴闁逞屽墰閺佽鐣烽幋锕€绠婚柡鍌樺劜閻忎線姊洪崜鑼帥闁哥姵顨婇幃姗€宕煎┑鎰瘜闂侀潧鐗嗘鎼佺嵁濮椻偓閺屾稖绠涢弮鎾光偓鍧楁煟濞戝崬娅嶇€规洘锕㈤、娆戝枈鏉堛劎绉遍梻鍌欑窔濞佳囨偋閸℃稑绠犻柟鏉垮彄閸ヮ亶妯勯梺鍝勭焿缂嶁偓缂佺姵鐩獮姗€宕滄笟鍥ф暭闂傚倷鑳剁划顖炪€冮崱娑栤偓鍐醇閵夈儳鍔﹀銈嗗笂閼冲爼鎮¢婊呯<妞ゆ梻鏅幊鍐┿亜椤愩垻绠婚柟鐓庢贡閹叉挳宕熼銈呴叡闂傚倷绀侀幖顐ゆ偖椤愶箑纾块柛妤冨剱閸ゆ洟鏌℃径濠勬皑闁衡偓娴犲鐓熼柟閭﹀幗缁舵煡鎮樿箛鎾虫殻闁哄本鐩鎾Ω閵夈儳顔掗柣鐔哥矋婢瑰棝宕戦幘鑸靛床婵犻潧顑嗛崑銊╂⒒閸喎鍨侀柕蹇曞Υ閸︻厽鍏滃瀣捣琚﹂梻浣芥〃閻掞箓宕濋弽褜鍤楅柛鏇ㄥ€犻悢铏圭<婵☆垵宕佃ぐ鐔兼⒒閸屾艾鈧绮堟笟鈧獮澶愭晸閻樿尙顔囬梺绯曞墲缁嬫垵顪冩禒瀣厱闁规澘鍚€缁ㄨ崵绱掗妸锝呭姦婵﹤顭峰畷鎺戭潩椤戣棄浜鹃柣鎴eГ閸ゅ嫰鏌涢幘鑼槮闁搞劍绻冮妵鍕冀椤愵澀绮剁紓浣插亾濠㈣埖鍔栭悡銉╂煛閸モ晛浠滈柍褜鍓欓幗婊呭垝閸儱閱囬柣鏃囨椤旀洟姊虹化鏇炲⒉閽冮亶鎮樿箛锝呭箻缂佽鲸甯¢崺鈧い鎺嶇缁剁偤鏌熼柇锕€骞橀柛姗嗕邯濮婃椽宕滈幓鎺嶇凹缂備浇顕ч崯顐︻敊韫囨挴鏀介柛顐犲灪閿涘繘姊洪崨濠冨瘷闁告洦鍓涜ぐ褔姊绘笟鈧埀顒傚仜閼活垱鏅堕鍓х<闁绘灏欐晥閻庤娲樺ú鐔煎蓟閸℃鍚嬮柛娑卞灱閸炵敻姊绘担渚敯闁规椿浜濇穱濠囧炊椤掆偓閻鏌¢崶鈺佹瀭濞存粍绮撻弻鐔兼倻濡櫣浠撮梺閫炲苯澧伴柡浣筋嚙閻g兘骞嬮敃鈧粻濠氭煛閸屾ê鍔滈柣蹇庣窔濮婃椽宕滈懠顒€甯ラ梺鍝ュУ椤ㄥ﹪骞冨鈧畷鐓庘攽閹邦厼鐦滈梻渚€娼ч悧鍡橆殽閹间胶宓佹慨妞诲亾闁哄本绋栫粻娑㈠籍閹惧厜鍋撻崸妤佺厽婵炴垵宕▍宥団偓瑙勬礃閿曘垽銆佸▎鎴濇瀳閺夊牄鍔庣粔閬嶆⒒閸屾瑧绐旀繛浣冲洦鍋嬮柛鈩冪☉缁犵娀鏌熼弶鍨絼闁搞儺浜跺Ο鍕⒑閸濆嫮鐒跨紓宥佸亾缂備胶濮甸惄顖炵嵁濮椻偓瀹曟粍绗熼崶褎鏆梻鍌氬€烽懗鍓佸垝椤栫偑鈧啴宕卞☉鏍ゅ亾閸愵喖閱囬柕澶堝劤閸旓箑顪冮妶鍡楃瑐闁煎啿鐖奸幃锟狀敍濠婂懐锛滃銈嗘⒒閺咁偊骞婇崘鈹夸簻妞ゆ劑鍨荤粻濠氭煙閻撳孩璐¢柟鍙夋尦瀹曠喖顢曢妶鍛村彙闂傚倸鍊风粈渚€骞栭銈嗗仏妞ゆ劧绠戠壕鍧楁煕濡ゅ啫鍓遍柛銈嗘礋閺屸剝寰勬繝鍕殤闂佽 鍋撳ù鐘差儐閻撶喖鏌熼柇锕€骞楃紒鑸电叀閹绠涢幘铏闂佸搫鏈惄顖氼嚕閹绢喖惟闁靛鍎抽鎺楁煟閻斿摜鐭嬪鐟版瀹曟垿骞橀懜闈涘簥濠电娀娼ч鍡涘磻閵娾晜鈷掗柛顐ゅ枎閸ㄤ線鏌曡箛鏇炍ラ柛锔诲幗閸忔粌顪冪€n亝鎹g悮锕傛⒒娴h姤銆冮柣鎺炵畵瀹曟繈寮借閸ゆ鏌涢弴銊モ偓鐘绘偄閾忓湱锛滃┑鈽嗗灥瀹曚絻銇愰悢鍏尖拻闁稿本鑹鹃埀顒勵棑缁牊绗熼埀顒勭嵁婢舵劖鏅搁柣妯垮皺椤斿洭姊虹化鏇炲⒉缂佸鍨甸—鍐╃鐎n偆鍘遍梺瑙勬緲閸氣偓缂併劏宕电槐鎺楀Ω閿濆懎濮﹀┑顔硷工椤嘲鐣烽幒鎴僵妞ゆ垼妫勬禍楣冩煟閹达絽袚闁搞倕瀚伴弻娑㈠箻閼碱剦妲梺鎼炲妽缁诲啴濡甸崟顖氬唨妞ゆ劦婢€缁墎绱撴担鎻掍壕婵犮垼鍩栭崝鏍偂閵夆晜鐓涢柛銉㈡櫅娴犳粓鏌嶈閸撴瑩骞楀鍛灊闁割偁鍎遍柋鍥煟閺冨洦顏犳い鏃€娲熷铏瑰寲閺囩偛鈷夐柦鍐憾閹绠涢敐鍛缂備浇椴哥敮锟犲春閳ь剚銇勯幒宥囶槮缂佸墎鍋ら弻鐔兼焽閿曗偓楠炴﹢鏌涘鍡曢偗婵﹥妞藉畷婊堝箵閹哄秶鍑圭紓鍌欐祰椤曆囧疮椤愶富鏁婇煫鍥ㄦ尨閺€浠嬫煕椤愮姴鐏柨娑樼箻濮婃椽宕ㄦ繝鍐ㄧ樂闂佸憡娲﹂崜娑溿亹瑜斿缁樼瑹閳ь剟鍩€椤掑倸浠滈柤娲诲灡閺呭爼顢欓崜褏锛滈梺缁橆焾鐏忔瑦鏅ラ柣搴ゎ潐濞叉ê煤閻旂厧钃熼柛鈩冾殢閸氬鏌涘☉鍗炵伇闁哥偟鏁诲缁樻媴娓氼垱鏁梺瑙勬た娴滄繃绌辨繝鍥х倞妞ゆ巻鍋撻柣顓燁殜閺岋繝宕堕埡浣圭€繛瀛樼矋缁捇寮婚悢鍏煎€绘俊顖濇娴犳挳姊洪柅鐐茶嫰婢т即鏌℃担绛嬪殭闁伙絿鍏橀獮瀣晝閳ь剛绮绘繝姘厸闁稿本锚閸旀粓鏌h箛搴g獢婵﹥妞藉畷婊堟嚑椤掆偓鐢儵姊洪崫銉バfい銊ワ躬楠炲啫顫滈埀顒€鐣烽悡搴樻斀闁归偊鍘奸惁婊堟⒒娓氣偓濞佳囨偋閸℃﹩娈介柟闂磋兌瀹撲焦鎱ㄥ璇蹭壕闂佸搫鏈粙鏍不濞戙垹绫嶉柟鎯у帨閸嬫捇宕稿Δ浣哄幗濠电偞鍨靛畷顒€鈻嶅鍥e亾鐟欏嫭绀冮柨鏇樺灲閵嗕礁鈻庨幋婵囩€抽柡澶婄墑閸斿海绮旈柆宥嗏拻闁稿本鐟х粣鏃€绻涙担鍐叉处閸嬪鏌涢埄鍐槈缂佺姷濞€閺岀喖寮堕崹顔肩导闂佹悶鍎烘禍璺何熼崟顖涒拺闁告繂瀚悞璺ㄧ磽瀹ヤ礁浜剧紓鍌欒兌婵敻鎯勯鐐靛祦婵せ鍋撶€规洘绮嶇粭鐔煎炊瑜庨弳顓㈡⒒閸屾艾鈧兘鎳楅崜浣稿灊妞ゆ牜鍋戦埀顒€鍟村畷鍗炩槈閺嶃倕浜鹃柛鎰靛枛闁卞洭鏌曟径鍫濆姢闁告棑绠戦—鍐Χ閸℃鐟愰梺鐓庡暱閻栧ジ骞冮敓鐙€鏁嶆繝濠傛噽閿涙粌顪冮妶鍡樷拻闁哄拋鍋婇獮濠囧礃閳瑰じ绨诲銈嗗姂閸ㄨ崵绮绘繝姘厵闁绘挸瀛╃拹锟犳煙閸欏灏︾€规洜鍠栭、鏇㈠Χ閸涙潙褰欓梻鍌氬€搁崐椋庣矆娓氣偓楠炴牠顢曢妶鍡椾粡濡炪倖鍔х粻鎴犲閸ф鐓曟俊銈呭暙閸撻亶鏌涢妶鍡樼闁哄备鍓濆鍕節閸曨剛娈ら梻浣姐€€閸嬫挸霉閻樺樊鍎愰柣鎾跺枛閺岀喖鏌囬敃鈧獮妤冪磼閼哥數鍙€闁诡喗顭堢粻娑㈠箻閾忣偅顔掗梻浣告惈閺堫剟鎯勯姘煎殨闁圭虎鍠栨儫闂侀潧顦崕鎶筋敊閹烘鐓熼柣鏂挎憸閻顭块悷鐗堫棦鐎规洘鍨块獮姗€鎳滈棃娑樼哎婵犵數濞€濞佳囶敄閸℃稑纾婚柕濞炬櫆閳锋帡鏌涢銈呮瀻闁搞劋绶氶弻鏇$疀閺囩倣銉╂煕閿旇骞楅柛蹇旂矊椤啰鈧綆浜濋幑锝囨偖閿曞倹鈷掑ù锝堝Г閵嗗啴鏌i幒鐐电暤鐎规洘绻堝鍊燁檨闁搞倖顨婇弻娑㈠即閵娿儮鍋撻悩缁樺亜闁惧繐婀遍敍婊冣攽閳藉棗鐏ョ€规洑绲婚妵鎰版偄閸忓皷鎷婚梺绋挎湰閼归箖鍩€椤掑嫷妫戠紒顔肩墛缁楃喖鍩€椤掑嫮宓佸鑸靛姈閺呮悂鏌eΟ鍨毢妞ゆ柨娲铏瑰寲閺囩偛鈷夌紓浣割儐閸ㄧ敻鈥旈崘鈺冾浄閻庯綆鍋嗛崢閬嶆⒑鐟欏嫭绶查柛姘e亾缂備降鍔忓畷鐢垫閹烘惟闁挎繂鎳庢慨锕€鈹戦纭峰伐妞ゎ厼鍢查悾鐑藉箳閹搭厽鍍靛銈嗗灱濡嫭绂嶆ィ鍐╃厽闁硅揪绲借闂佹悶鍊曠€氫即寮诲☉銏犵闁肩⒈鍓﹀Σ顕€姊洪幖鐐插缂佽鍟存俊鐢稿礋椤栨艾鍞ㄥ銈嗗姦濠⑩偓缂侇喖澧庣槐鎾存媴閹绘帊澹曞┑鐘灱閸╂牠宕濋弽顓熷亗闁靛鏅滈悡娑㈡煕閵夈垺娅呭ù鐘崇矒閺屽秷顧侀柛鎾寸懇楠炴顭ㄩ崨顓炵亰闂佸壊鍋侀崕閬嶆煁閸ヮ剚鐓熼柡鍐ㄦ处椤忕姵銇勯弮鈧ú鐔奉潖閾忕懓瀵查柡鍥╁仜閳峰鏌﹂崘顔绘喚闁诡喗顭堢粻娑㈡晲閸涱厾顔掔紓鍌欐祰妞村摜鏁敓鐘叉槬闁逞屽墯閵囧嫰骞掑鍥舵М缂備礁澧庨崑銈夊蓟閻斿吋鐒介柨鏇楀亾妤犵偞锕㈤弻娑橆潨閸℃洟鍋楀┑顔硷攻濡炶棄鐣峰鍫濈闁瑰搫绉堕崙鍦磽閸屾瑦绁版い鏇嗗洤鐤い鎰跺瘜閺佸﹪鐓崶銊﹀皑闁衡偓娴犲鐓曟い鎰Т閻忣亪鏌ㄥ☉妯肩婵﹥妞藉畷銊︾節閸愩劎妯傞梻浣告啞濞诧箓宕滃☉婧夸汗鐟滄柨顫忕紒妯肩懝闁逞屽墴閸┾偓妞ゆ帒鍊告禒婊堟煠濞茶鐏¢柡鍛埣椤㈡瑩宕滆閿涙粓姊虹紒姗嗙劸閻忓繑鐟﹂弲銉╂煟鎼淬値娼愭繛鍙壝叅闁绘梻鍘ч拑鐔兼煕閳╁喚娈㈤柛姘儔閺屾稑鈽夐崡鐐典紘闂佸摜鍋熼弫璇差潖缂佹ɑ濯村〒姘煎灡閺侇垶姊虹憴鍕仧濞存粍绻冪粚杈ㄧ節閸パ呭€炲銈嗗坊閸嬫捇鏌i鐕佹疁闁哄矉绻濆畷鍫曞煛娴e湱鈧厽绻涚€涙鐭嬬紒顔芥崌瀵鎮㈤崗鐓庘偓缁樹繆椤栨繃顏犲ù鐘虫尦濮婃椽鏌呴悙鑼跺濠⒀傚嵆閺屸剝鎷呯粵瀣闂佷紮绲块崗姗€鐛€n喗鏅濋柍褜鍓涚划缁樼節濮橆厾鍘搁梺绋挎湰閿氶柛鏃€绮撻弻锝堢疀鎼达絿鐛㈠┑顔硷攻濡炶棄鐣峰鍫熷殤妞ゆ巻鍋撻悽顖樺劦濮婃椽宕妷銉愶絾銇勯妸銉含妤犵偛鍟~婊堝焵椤掆偓閻g兘鎮℃惔妯绘杸闂佸綊鍋婇崢濂告儊濠婂牊鈷掑〒姘e亾婵炰匠鍥ㄥ亱闁糕剝锕╁▓浠嬫煙闂傜鍏岀€规挷鐒﹂幈銊ヮ渻鐠囪弓澹曢梻浣告惈閺堫剛绮欓弽顐や笉婵炴垯鍨圭猾宥夋煙閹冨辅闁稿鎹囧畷绋课旀担鍝勫箺婵犵數鍋為崹闈涚暦椤掆偓閳诲秴顓奸崶锝呬壕閻熸瑥瀚粈鍐煥閺囨ê鐏查柕鍡曠閳诲酣骞嬪┑鍥┾偓鎶芥煛婢跺﹦澧戦柛鏂挎捣缁棃鏌嗗鍡忔嫽闂佺鏈悷褏绮i弮鈧换娑欐媴閸愬弶澶勯柛瀣儔閺屾盯鍩勯崘顏佹缂備胶濮锋繛鈧柡宀€鍠栧鍫曞垂椤旇偐瀵奸梻浣规偠閸庣儤绂嶇捄浣曠喖宕熼娑掓嫼闂佸憡绻傜€氼噣鎮炵捄銊х=鐎广儰绀佹禍鍓х磽閸屾瑨鍏屽┑顔炬暬閹嫰顢涢悙闈涚ウ濠殿喗銇涢崑鎾垛偓瑙勬礃缁秶绮悢鐓庣倞鐟滃酣寮抽銏♀拻闁稿本鑹鹃埀顒傚厴閹虫宕滄担绋跨亰濡炪倖鐗滈崑鎴﹀焵椤掆偓閸熸潙鐣烽崡鐐╂闁哄秲鍊曟禍楣冩煕閹伴潧鏋涢梺鍗炴喘閺屾洘寰勯崼婵嗗Б闂佸憡妫戠粻鎴︹€旈崘顔嘉ч柛鈩冾殘閻熸劙姊洪悡搴℃毐闁绘牕銈搁獮鍐晸閻欌偓閺佸秵绻濇繝鍌涘櫧闁挎稒绮岄—鍐Χ閸℃ǚ鎷婚梺鍝勬媼閸嬪﹪鐛繝鍥х闁崇懓銇樼花璇差渻閵堝棗濮傞柛銊ㄥ吹缁粯绻濆顓犲幍闂佺粯鎸哥€涒晝鎷归敓鐘崇厵闁告瑥顦扮亸锔锯偓瑙勬礈閸犳牠銆侀弴銏犖ч柛娑欐綑瑜版瑩姊婚崒姘偓鎼佸磹妞嬪海鐭嗗〒姘e亾妤犵偞鐗犻、鏇㈠Χ閸℃ぞ绮℃俊鐐€栭崝褏绮婚幋鐘差棜闁秆勵殕閻撴洘淇婇妶鍛殭闁告捇浜堕弻娑㈠Χ閸℃顦伴梺鍝勫閸撴繂顕ラ崟顒傜瘈闁告洦鍓涘▓銈夋⒒娴e鈧偓闁稿鎸搁湁闁绘ê妯婇崕鎰版煟閹捐泛鏋涢柡宀€鍠栭弻鍥晝閳ь剟鐛Δ鍐<闁煎摜鏁搁崣鈧梺璇″枟椤牏绮诲☉銏犵闁惧浚鍋呴鎺楁⒒娴e憡鎯堥柡鍫墴閹嫰顢涘鐓庢闂佸湱铏庨崰鏍ㄥ劔闂備線娼чˇ顓㈠磿閹剁瓔鏁婇柟鐑橆殕閻撶喖鏌i弬鎸庢喐闁活厼顑呴…鍧楁偡閻楀牜妫﹂悗瑙勬礃閸ㄥ潡鐛鈧幊婊堟濞戞鍝庡┑鐘垫暩婵炩偓婵炰匠鍥舵晞闁糕剝绋戠壕濠氭煏婵炵偓娅嗛柍閿嬪浮閺屾盯顢曢妶鍛€婚梺鎼炲妺缁舵岸寮婚弴锛勭杸闁哄洨鍊i妷鈺傜厱闁挎棁顕ч獮妤呮煕韫囨梻鐭婃い顏勫暟閳ь剨缍嗘禍婵嬪箲閿濆洦鍋栭柨鏇炲€归埛鎺懨归敐鍫澬撻柕鍡楀暣閺岋綁骞掗悙鐢垫殼閻庤娲樼换鍫濐嚕閸婄噥妾ㄩ梺鎼炲€栭〃濠囧蓟濞戙垹鍗抽柕濞垮劗閸嬫捇鎮╃紒妯轰簻闂佹儳绻愬﹢閬嶆晬濠婂啠鏀介柍钘夋閻忋儳鈧娲戠徊濠氬Φ閹扮増鍋勯柛蹇撶毞閹峰姊虹粙鎸庢拱闁煎綊绠栭崺鈧い鎺戝濡垹绱掗鑲╁缂佹鍠栭崺鈧い鎺戝瀹撲礁顭块懜闈涘闁哄懏鎮傞弻锝呂熼崹顔炬濡炪倖鏌ㄥú顓烆潖閾忕懓瀵查柡鍥╁仜閳峰绱撴担鍓插剱闁搞劎鏁婚垾鏃堝礃閳哄喚娴勯柣搴秵閸嬪棝宕㈤柆宥嗏拺閻熸瑥瀚欢鏌ユ煕濮橈絽浜剧紓鍌欓檷閸斿繐鐣烽悽鍨潟闁圭儤顨呮儫闂佹寧绻傞幊搴㈡叏閿曗偓閳规垿顢欑涵宄颁紣濡炪値鍘奸崲鏌ユ偩閻戣棄绠抽柟鎼幗閸嶉潧顪冮妶鍡楃伇婵☆偄瀚粋宥嗐偅閸愨晝鍘介梺纭呮彧缁插€燁暱闂備焦鎮堕崐鏇犫偓姘嵆瀵鈽夐姀鐘殿啋闂佽偐鈷堥崜锕€危椤曗偓濮婃椽骞栭悙鎻掝瀴缂備浇顕ч崯瀛樹繆閻㈢绀嬫い鏍ㄨ壘閸炪劌顪冮妶鍡楀Е婵犫懇鍋撶紓渚囧枛婢у海妲愰幘瀛樺闁圭粯甯婃竟鏇炩攽閻橆喖鐏遍柛鈺傜墵瀹曟繈寮介鐔蜂簵闂侀潧顦弲婊堟偂濞戙垺鐓曢柕澶堝灪濞呭懎霉閻樺磭鐭掗柡灞界Х椤т線鏌涢幘瀵告噰妤犵偞顨呴…銊╁川椤撶偟浜伴梻浣稿閸嬩線宕曢柆宥嗙厑闁搞儺鍓氶悡鐔兼煛閸愩劍澶勬い蹇曞У閵囧嫰寮埀顒€煤閻斿娼栭柧蹇曟嚀鐎垫煡鏌¢崶鈺佷粶闁冲嘲顦甸弻锕傚礃椤旂粯鍠氶梺璇″枟椤牏绮诲☉銏℃櫜闁告侗鍘鹃鎺旂磽閸屾瑦绁板鏉戞憸閺侇噣鏁撻悩鍙夋К闂侀€炲苯澧柕鍥у楠炴帒顓奸崶鑸敌滅紓鍌欑婢у酣宕戦妶澶婅摕闁绘柨鍚嬮悞浠嬫煥閺囨浜惧Δ鐘靛仦閿曘垽寮诲☉姗嗘建闁糕剝娲熼崑妤€鈹戦纭锋敾婵$偠妫勯悾宄邦煥閸繄顔岄梺鐟版惈缁夊爼宕欓崷顓犵=闁稿本鐟︾粊鐗堛亜閺囧棗娲ら悿顔姐亜閹拌泛鐦滈柡浣革躬閻擃偊宕堕妸锕€鐨戦梺琛″亾濞寸姴顑嗛悡鏇熴亜閹邦喖孝闁诲浚浜弻銊モ槈濡偐顔掑┑顔硷攻濡炶棄鐣烽妸锔剧瘈闁告劑鍔庡Ο鍌炴⒒娴e憡鍟炴繛璇х畵瀹曟粌鈽夊┃澶告睏閻熸粍鏌ㄩ~蹇曠磼濡偐鎳濋梺閫炲苯澧撮柛鈹惧亾濡炪倖甯掗崐鍛婄濠婂牊鐓犳繛鑼额嚙閻忥繝鏌¢崨顓犲煟妞ゃ垺鐟╁畷婊嗩槾闁挎稒绮撳铏圭磼濮楀棛鍔搁柣蹇撶箲閻燂箓寮查妷鈺傜厽閹兼番鍊ゅ鎰箾閸欏顏嗗弲闂佺粯姊婚崢褔鎷戦悢鍏肩厱闁斥晛鍠氬▓銏ゆ煕濮橆剦鍎旈柡灞剧☉閳藉宕¢悙鍏哥礃闂備礁鎽滈崑鐔煎极鐠囧樊娼栫紓浣股戞刊鏉戙€掑鐓庣仭闁轰緡鍨跺铏规喆閸曨兙浠ф繛瀛樼矋缁诲啰绮氭潏銊х瘈闁搞儜鍛偓鐐差渻閵堝棗鍧婇柛瀣崌閺岋綁顢橀悤浣圭杹闂佸搫鐭夌换婵嗙暦閸洖鐓涘ù锝呮贡閳ь剦鍘界换娑氣偓娑欘焽閻绱掗鑺ュ磳鐎殿喖顭烽幃銏ゅ礂閻撳簶鍋撶紒妯圭箚妞ゆ牗绻冮鐘裁归悩铏唉婵﹥妞介弻鍛存倷閼艰泛顏繝鈷€鍌氬祮闁哄备鍓濋幏鍛驳鐎n亝顔勯梻浣风串缁插潡宕楀鈧悰顔锯偓锝庡枟閺呮繈鏌嶈閸撴稓鍒掔紒妯肩瘈婵﹩鍘鹃崢鎼佹⒑缁嬫寧婀伴柨姘舵煕閺冣偓缁捇寮婚敐鍫㈢杸閹艰揪绲块悰銏犫攽椤旂》鏀绘俊鐐舵閻e嘲顭ㄩ崼鐔锋濡炪倖宸婚崑鎾绘偨椤栨ê鍔︽慨濠冩そ瀹曨偊濡烽妷鎰剁稻閵囧嫰濡搁妷顖濆惈濡ょ姷鍋涢崯顐︼綖濠婂牆鐒垫い鎺嗗亾闁伙絿鍏橀幃鈩冩償濡粯鏉搁梻浣哥秺閸嬪﹪宕㈡總鍛婂剨婵犲﹤鐗婇埛鎺戙€掑锝呬壕濠电偘鍖犻崶銊ヤ罕闂佺硶鍓濋敃鈺佲枔娴犲鐓欓梻鍌滎棎閸忓瞼鈧鎸烽悞锕傚箞閵娿儺娓婚悹鍥紦婢规洟姊绘担鍛婃儓闁哄牜鍓涚划娆撳冀椤愩倓绗夊┑鐐村灟閸ㄥ湱鐚惧澶嬬厵闁诡垎鍐ㄨ緟闂佺顑嗛幑鍥х暦缁嬭鏃€鎷呴崫鍕濠电姷鏁搁崑鐐哄垂闂堟稓鏆︽い鎺嗗亾闁宠绉撮濂稿炊閿濆懍澹曢柣鐔哥懃鐎氼厾绮堥崘顔界叆闁哄洦锚閻忔煡鏌曢崱鏇狀槮闁宠閰i獮瀣攽閸モ斁鍋撻幎鑺ョ厸濠㈣泛锕︽晶鎴︽煕閺傛寧鎹g紒顔芥閺屽棗顓奸崱蹇斿闂備胶顭堥張顒勬偡瑜忕划锝夊籍閳ь剛鎹㈠☉娆愬闁告劕寮舵径鍕煕鐎n亶鍎旈柡灞剧洴閸╁嫰宕橀浣诡潔缂傚倷鑳舵慨閿嬬箾閳ь剟鏌″畝鈧崰鏍ь嚕閸洖鍨傛い鏃囧亹鐎靛ジ姊绘担瑙勫仩闁稿海鍎ょ粋宥囨崉娴f洜鍠栧畷鐔碱敍濞戞帗瀚奸梻浣告啞缁诲倻鈧凹鍣i幃鐐垫崉閵娧咃紳閻庡箍鍎扮粈浣圭閸撗呯=闁稿本鐟ㄩ崗灞解攽椤旂偓鏆柟顖氬椤㈡盯鎮欓棃娑氥偊婵犳鍠楅妵娑㈠磻閹惧灈鍋撶憴鍕缂侇喖绉剁划顓㈡偄閻撳海鍊為悷婊冮叄瀵娊顢橀姀鈾€鎷婚梺绋挎湰閼归箖鍩€椤掑倸鍘撮柟铏殜瀹曟粍鎷呯粙璺ㄤ喊婵$偑鍊栭悧婊堝磻閹达箑鐒垫い鎺嗗亾闁哥喐娼欓悾鐑藉础閻愨晜顫嶉梺鍝勭Р閸婃洘绂嶆ィ鍐╃厱闁逛即娼ч弸娑㈡⒑閸楃偞鍠橀柡灞炬礃瀵板嫰宕煎┑鍡椥戦梻浣告啞濡垹绮婚幋锔光偓鏃堝礃椤斿槈褔鏌涢埄鍐炬畼闁荤喐鍔欏娲偂鎼粹剝姣愰梺缁樼墪閵堟悂鐛崘顔芥櫢闁绘瑢鍋撻柡浣哥У缁绘繃绻濋崒娑樻闂佹寧绋掔划宀勨€旈崘顔嘉ч柛鈩兦氶幏濠氭⒑閸濆嫭濯奸柛瀣躬閻涱喗绻濋崶褏顦ㄩ梺宕囨嚀閵囨鑺辩拠宸富闁靛牆妫楁慨鍌炴煕閵娿劌鍚圭紒顔剧帛缁绘繂顫濋鐘插箥闂備胶绮幐鍝モ偓娑掓櫇閹峰綊鏁撻悩宕囧幍闂佸憡鐟ラˇ鎵焊閿旈敮鍋撶憴鍕闁哥姵鐗犻妴渚€寮撮姀鐘栄囨煕濞戞瑦缍戠憸鐗堢懇濮婂宕掑顑藉亾閹间礁纾瑰瀣捣閻棗銆掑锝呬壕濡ょ姷鍋為悧鐘汇€侀弴銏犖ч柛鈩冦仦缁剝淇婇悙顏勨偓鏍礉瑜忕划濠氬箣閻樺樊妫滈梺绉嗗嫷娈曢柣鎾存礃娣囧﹪濡堕崨顓熸闂佸憡鎹囨禍鍫曞蓟濞戙垹围闁糕剝顭囬ˇ浼存⒑閸濆嫬顦柛鎾寸箓椤曘儵宕熼鍌滅槇闂佸憡娲﹂崜娑樷枔閵堝鈷掑ù锝咁潟閳ь兘鍋撻梺绋款儐閹告悂婀侀梺缁樏Ο濠囧磿閹扮増鐓熼柟鎹愭硾閺嬫盯鏌″畝鈧崰鏍蓟閸ヮ剚鏅濋柍褜鍓熼悰顔嘉旈崘顏嗭紲闂佺厧鎽滈弫鎼佸矗閳ь剟姊虹拠鈥虫灍妞ゎ厼鐗忕划璇测槈閵忕姷顔掗梺鎯ф禋閸嬪懘顢欓幒妤佲拻濞达絽鎲¢幆鍫ユ煛閸偄澧撮柟顖氬椤㈡稑顫濋悡搴㈩吙闂備礁婀遍搹搴ㄥ窗閺嶃劌鍔旈梻鍌欑窔濞佳囁囬銏犵?闁瑰墎鐡旈弫濠囨煙閻戞﹩娈曢柣鎾跺枛閺岋綁寮幐搴㈠枑闂佹椿鍘奸鍛粹€﹂崸妤佸仭闁绘鐗滃Λ锕傛倵鐟欏嫭绀冮柛銊ユ健閻涱喖顫滈埀顒勫箠濠婂牊顥堟繛鎴烆焽閸濆骸鈹戦悩鍨毄濠电偐鍋撳┑鐐板尃閸ヨ埖鏅為梺绯曞墲缁嬫垹澹曟繝姘厪濠电偟鍋撳▍鍡涙煃闁垮娴柡灞剧洴椤㈡洟濡堕崨顔锯偓濠氭⒑閹肩偛濡虹紒鑸靛哺瀵寮撮敍鍕澑闂佸搫娲ㄩ崐锝夊Ψ閳哄倻鍘遍梺鎸庢椤曆囩嵁濡ゅ懏鐓曢煫鍥ㄦ⒒閻﹥銇勯鍕殶闁逞屽墾缂嶅棙绂嶅┑瀣闁挎繂娲﹂崑鏍煥閺囩偛鈧綊鍩涢幒鎳ㄥ綊鏁愰崼婢捇鏌曢崱妤€鏆i柡宀嬬秮楠炴帡鎮欓悽鍨闁诲氦顫夊ú妯兼崲閸繍鍤曢柛濠勫櫏濡俱劑姊洪幖鐐测偓鏍€冩繝鍥ц摕婵炴垯鍨归崡鎶芥煏婵炲灝鍔楅柛瀣崌閹晝绱掑Ο杞扮盎闂備焦鍎崇换鎰耿闁秵鏅繝濠傚暊閺€浠嬫煃閽樺顥滈柣蹇嬪劤閳ь剝顫夊ú鎴犲緤婵犳艾桅闁规壆澧楅崑鍕煕韫囨挾姣為柟宄邦煼濮婅櫣绮欓幐搴㈡嫳闂佺厧缍婄粻鏍春閳ь剚銇勯幒鎴濐伌婵☆偅鍨圭槐鎺楊敊閼测晛顤€缂備焦顨堥崰鏍春閳ь剚銇勯幒鎴濐伀鐎规挷绀侀…鍧楁嚋闂堟稑顫嶉梺鍝勬噺閹倿寮婚敐鍛傜喖宕归鐐嚄婵$偑鍊栭弻銊ッ洪鐑嗘綎闁惧繒鎳撶€垫煡鏌¢崶鈺佷粶闁冲嘲顦辩槐鎾存媴閸撴彃鍓遍梺鎼炲妿閺佸鍨鹃弮鍫濈闁冲搫鍠氬ù鍕煟鎼搭垳绉甸柛瀣瀹曘垽鏌嗗鍡忔嫼闁荤喐鐟ョ€氼厾娆㈤弻銉︾厱婵﹫绲芥禍鍓х磽閸屾瑩妾烽柛鏂跨箰閻g兘鎮介崹顐綗闂佸湱鍎ら〃鍛劔闂備焦瀵х换鍌炲箠鎼淬垺鍙忛柨鏇楀亾闁宠鍨块、娆戞兜瀹勯绱f俊鐐€ら崢濂稿床閺屻儲鍋╅柣鎴f缁犳娊鏌熼幖顓炲箺闁稿秹娼ч—鍐Χ閸℃浼囧┑鈽嗗亜鐎氼厾绮嬪鍡愬亝闁告劏鏅濋崢浠嬫⒑绾懏褰х紒鎻掆偓鐕佹毐闂傚倷鐒﹂幃鍫曞磹閺囩姭鍋撳顐㈠祮鐎殿喛顕ч埥澶愬閻樻鍟嬮梻浣藉亹閳峰牓宕滈敃鈧嵄妞ゆ洍鍋撴慨濠冩そ楠炴牠鎮欓幓鎺濈€寸紓鍌欐祰椤曆囧疮鐎涙ü绻嗛柣銏㈩焾缁€瀣亜閺嶃劏澹橀柛鐐妼椤啴濡堕崱妤€袝濠电姭鎳囬崑鎾剁磽娓氬洤鏋涘褍娴峰Σ鎰板箻鐎涙ê顎撻梺鍦帛鐢﹥绔熼弴鐐╂斀闁绘﹩鍠栭悘閬嶆煕閳哄倻澧电€规洘绻堝浠嬵敇閻旇渹绨甸梻渚€娼чˇ顐﹀疾濠婂牊鍋傛繛鎴欏灪閻撴洟鏌曟径鍫濈仾婵炲懎鎳庨湁闁绘ê纾惌鎺楁煛鐏炵晫啸妞ぱ傜窔閺屾盯骞樼€靛憡鍣板Δ鐘靛仦椤ㄥ懘鈥﹂妸鈺佸窛妞ゆ挾鍋熸禍浼存⒒娴g顥忛柛瀣╃窔瀹曟洟鏌嗗鍡欏帒闂佹悶鍎洪崜姘舵偂閻斿吋鐓涢柛鎰╁妽婢跺嫭銇勮箛鏇炐i柕鍥у瀵噣鍩€椤掆偓鐓ら柣鏂款殠濞兼牠鏌ц箛鏇熷殌閻庡灚鐓¢弻锟犲炊閳轰椒绮堕梺鍐插槻椤︾敻寮婚敃鍌氱妞ゆ梻绮崰姘舵⒑鐠団€虫灍妞ゎ厼鐗忕划璇测槈閵忊剝娅滈梺鍛婁緱閸橀箖顢欓幒鏃傜=闁稿本鐟︾粊鏉款渻閺夋垶鎲搁柡渚囧櫍閺佹捇鎮╅崣澶嬓氶梻渚€鈧偛鑻晶顖炴煏閸パ冾伃妤犵偞甯掗濂稿炊閼告晫婊呯磽閸屾瑧顦﹀褍閰e畷鎴﹀Χ婢跺﹨鎽曢梺缁樻煥閸氬鎮炴禒瀣叆闁哄洦顨呮禍鎯旈悩闈涗沪闁挎洏鍨藉璇测槈濮楀棙寤洪梺绯曞墲濞茬喖宕戝Δ鈧埞鎴︻敊绾攱鏁惧┑锛勫仩濡嫰鎮惧畡閭︾叆闁割偅绻勯宀勬⒑閻熺増鎯堢紒澶婄埣瀹曟瑩宕烽鐘碉紳闂佺鏈悷锔剧矈閻楀牄浜滈柡鍥ф濞层倝鎮块濮愪簻闁规媽娉涢惁婊堟煛娴i潻韬柣鎿冨亰瀹曞爼濡搁敃鈧惃鎴︽⒑鐞涒€充壕婵炲濮撮鍡涙偂閺囩喆浜滈柟閭﹀枛瀛濋梺璇叉禋娴滎亪寮婚妸銉㈡婵☆垵鍋愰鎺戔攽椤旂》鏀绘俊鐐舵閻g兘濡搁敂鍓х槇闂佸憡鍔戦崝搴∥熼崒鐐粹拻濞达絽鎲¢崯鐐寸箾鐠囇呯暤鐎规洘绮岄埥澶娾攦婢跺憡鐫忛柣鐔哥矋閺屻劑锝炶箛鏇犵<婵☆垵鍋愰幊婵嬫⒑闁偛鑻晶鎾煕閳规儳浜炬俊鐐€栫敮鎺楀磹閸涘﹦顩锋繝濠傜墛閻撶姵绻涢懠棰濆殭闁诲骏绻濋弻锟犲川椤撶姴鐓熷銈冨灪閻熲晛鐣峰鍡╂Ь闂佹寧绋掔划鎾愁潖閾忓湱纾兼慨妤€妫涢崝鎼佹煟韫囨挾绠查柣鐕傜畵瀵煡濡烽埡鍌滃幗闁瑰吋鐣崐銈咁焽閹邦厾绠鹃柛娆忣棦椤忓棗寮查梻浣虹帛濮婂宕㈣閹锋垿鎮㈤崗鑲╁幈闂佹枼鏅涢崰姘枔閵忋倖鐓曟慨姗嗗墻閸庢棃鏌$仦鍓р槈闁宠棄顦靛畷锟犳倷閸忓摜绀冮梻鍌欑閹芥粓宕戦悢鐓庢瀬閻犲洤妯婂鏍磽娴h偂鎴炲垔閺夋垯鈧帒顫濋悡搴d画闂佽桨绶¢崹璺侯潖閾忚鍠嗛柛鏇ㄥ厵娴犙勭箾鐎涙鐭嬬紒璇插暟缁碍娼忛妸褏鐦堥梺鎼炲劀閸涱厸鍋撻悙宸富闁靛牆妫楅崸濠囨煕鐎n偅宕岄柡宀嬬秮椤㈡﹢鎮ゆ担鍦澒闂備礁鎼惌澶屾崲濠靛棛鏆﹂柛顐f礀閻撴稑霉閿濆懏璐¢柍褜鍓﹂崢鐣屾崲濞戞埃鍋撳☉娆樼劷闁活厼顑囩槐鎺楊敊閼恒儱纾抽悗娈垮枛椤兘骞冮姀銈呯闁绘挸绨堕崑鎾剁磼濡湱绠氬銈嗙墬缁诲啴顢旈悩瑁佸綊鎮╅搹顐㈠攭濠殿喖锕ュ浠嬪蓟閸涘瓨鍊烽柤鑹版硾椤忣厽绻濋埛鈧崒姘ギ闂佸搫澶囬崜婵嬪箯閸涱垳椹抽悗锝庝簼椤斿嫰姊绘担椋庝覆缂佹彃娼″畷妤€顫滈埀顒勬偘椤旈敮鍋撻敐搴℃灍闁哄懏绻堥弻宥堫檨闁告挻绋撻崚鎺旂磼濡偐鐦堝┑顔斤供閸橀箖宕㈤幖浣光拺缂佸瀵у﹢浼存煥濮樿埖鐓曢柡鍐e亾缂侇喗鎹囧濠氭晲閸垻鏉搁柟鑹版彧缁插潡鎮伴姀鐘斀妞ゆ梻銆嬮弨缁樹繆閻愯埖顥夐柣锝呭槻椤劑宕奸悢閿嬵吇婵$偑鍊栧濠氬磻閹剧粯鍋ㄦい鏍崝锔芥叏婵犲啯銇濈€规洦鍋婃俊鐑藉Ψ閹板墎绋婚柕鍥у婵℃悂濡烽婵嗘儓婵°倗濮烽崑娑㈠疮椤愶讣缍栨繝濠傜墕閻掑灚銇勯幒鍡椾壕闂佷紮绲块崗姗€骞冮埄鍐╁劅婵☆垳绮弶鎼佹⒒娴e摜绉洪柛瀣躬瀹曘垺绺介崨濠傚墾濠电姴锕ら悧濠囧煕閹烘垯鈧帒顫濋敐鍛婵犵數鍋橀崠鐘诲炊閵娿儰缃曢梻浣虹《閸撴繈鏁冮埡浣叉灁濞寸姴顑嗛悡娆撴⒒閸屾粠妫庨柛蹇撶灱閳ь剝顫夐幐鐑芥倿閿曞倸绠為柕濞垮労濞撳鎮归崶顏勭处濠㈣娲熷缁樻媴閸涘﹥鍎撻梺鍝勭墱閸撴稓鍒掑▎鎾冲唨妞ゆ劑鍊撶粭澶娾攽閻愭潙鐏熼柛銊ユ贡閻氭儳顓兼径瀣幍闂佽鍨庨崘銊ㄧ窡闂備胶顭堥鍡涘箲閸パ呮殾缂佸顕抽弮鈧幏鍛村传閸曨偆顔戞繝鐢靛Х閺佹悂宕戦悙鍝勫瀭闂傚牊绋撻弳锔姐亜閹哄棗浜鹃梺瀹狀嚙缁夋挳顢樻總绋跨倞闁挎繂鎳嶆竟鏇㈡煟閻斿摜鎳冮悗姘煎幘缁牓宕橀鐣屽弳闂佸搫娲﹂敋闁诲繑鐓¢弻鏇㈠幢閺囩媭妲梺瀹狀嚙闁帮綁鐛€n亖鏀介柛銉㈡杹閸嬫捇骞庨懞銉у幐婵犮垼娉涢敃锔芥櫠閹达附鐓曢柡鍌涘閹癸絿绱掗鑺ヮ棃闁哄苯妫楅濂稿幢韫囨柨顏洪梻鍌欒兌椤牓寮甸鍕仭鐟滃繒鍒掗敐澶婄睄闁逞屽墰閹广垹鈽夊▎鎰€撻梺鍛婂姇瀵埖寰勯崟顖涚厱閻庯綆浜堕崕鏃堟煛鐏炲墽娲撮柛鈺佸瀹曟﹢顢旀担璇℃綌缂傚倸鍊烽懗鑸垫叏闁垮绠鹃柍褜鍓熼弻鈥崇暆閳ь剟宕伴弽褜鍤曢柛顐f礀閸ㄥ倹銇勯弮鍥т汗閻庨潧銈稿缁樻媴鐟欏嫬浠╅梺绋挎捣閸庛倗绮嬪鍥ㄥ磯濞达絾娲滈崰鏍х暦閻旂⒈鏁嶆繛鎴炲笚鐎氬ジ姊绘担鍛婂暈缂佽鍊婚埀顒佸嚬閸o綁骞冮悙鍨磯闁靛ě鍜冪闯闁诲骸绠嶉崕鎵矆娴e湱顩查柛鎾楀懐锛濋梺绋挎湰閻熴劑宕楃仦瑙f斀妞ゆ梻鍋撻弳顒勬煙椤栨艾顏い銏$洴閹瑩妫冨☉姘ュ亰濠电姵顔栭崰妤呭Φ濞戙垹纾婚柟鎯х亪閸嬫挾鎲撮崟顒傤槰缂備緡鍠栫粔鍓佸垝椤撱垺鍋勯柣鎾虫捣閸婄偤鎮峰鍐弰鐎殿喗濞婇、姗€濮€閳锯偓閹峰姊虹粙鎸庢拱闁煎綊绠栭崺鈧い鎺戝€搁崢鎾煙閾忣偒娈滅€规洘绮嶉幏鍛矙鐠恒劋鍠婂┑锛勫亼閸婃牠鎮у鍫濈;闁硅揪绠戦悞鍨亜閹哄棗浜鹃梺鍝ュ枑濞兼瑩鎮鹃悜钘夌闁绘劏鏅滈~宥夋⒑閸濆嫮袪闁稿﹥娲樼粋宥嗐偅閸愨晝鍘遍梺閫涘嵆濞佳囧几濞戙垺鈷戦柛妤冨仦閸犳﹢鏌$仦鐐鐎垫澘瀚板畷鐓庘攽閸℃ぅ鎴︽⒒娴e憡鍟炴俊顐e灩缁骞嬮敂鍏夊亾閺冨牆绀冩い鏂挎瑜旈弻娑㈠焺閸愮偓鐣奸梺鑽ゅ枑閸旀瑥顫忓ú顏呭亗閹肩补鍓濆В鎰版⒑缂佹澧柕鍫熸倐閻涱噣宕橀鑺ユ闂佺粯鐟㈤崑鎾绘煛娴e摜校缂佺粯绻冪换婵嬪磼濞戞ɑ顏ら梻浣瑰缁嬫帞鍒掑畝鍕ㄢ偓鏃堝礃椤斿槈褔鏌涢埄鍏︽岸骞忔繝姘拺闁告繂瀚刊濂告煕鐎n亷韬柣娑卞枟缁绘繈宕惰椤︺劑姊哄畷鍥ㄥ殌闁靛洦顭囬懞杈╂嫚瀹割喗瀵岄梺闈涚墕濡鎱ㄩ崒鐐寸厱闁靛鍔岄崥鍦磼椤斿墽甯涚紒缁樼箓椤繈顢橀悩鎻掔闂傚倷鑳剁划顖炲箰閸濄儮鍋撳☉鎺撴珖闁瑰嘲缍婇弫鎾绘偐瀹曞洤骞嶉梻浣告啞閻熴儵藝閹殿喕鐒婇柨鏃堟暜閸嬫挾鎲撮崟顒傤槶闂佸摜濮甸悧鐘诲Υ娓氣偓瀵挳濮€閻樻爠鍥ㄧ厱婵炴垶鐟︾紞鎴犳喐閻楀牏鎳囨慨濠傤煼瀹曟帒顫濋钘変壕闁归棿绀佺壕鐟邦渻鐎n亝鎹i柣顓炴閵嗘帒顫濋敐鍛婵°倗濮烽崑鐐烘偋閻樻眹鈧線寮撮姀鐘栄囨煕閳╁啨浠︾紒顔瑰墲娣囧﹪鎮欓鍕ㄥ亾閺嶎厼绀夌憸蹇曞垝婵犳艾绠i柣妯烘▕濡粓姊虹粔鍡楀濞堟洟鏌i幘瀛樼濞e洤锕俊鍫曞川椤撶喐顔勯梻浣告啞閹瑰洦绂嶉崼鏇炶摕婵炴垯鍨瑰洿闂佺硶鍓濋…鍥囨导瀛樷拺闁告繂瀚ˇ顒勬煕閹惧绠撴い鏇樺劦瀹曠喖顢楅崒婊呮闂備礁鎲″ú锕傚礈濞戞ǚ鏋旈柕鍫濐槹閳锋帒霉閿濆拋娼熼柍褜鍏橀崑鎾绘⒑缁嬫鍎愰柟鍛婃倐濠€渚€姊虹紒妯忣亜螣婵犲洤纾块柟鎵閻撶喖鏌熼幑鎰【闁哄鐩弻鈥崇暆閳ь剟宕伴弽顓炶摕闁搞儺鍓氶弲婵嬫煃瑜滈崜鐔兼偘椤斿槈鏃堝礃椤忓棴绱查梻浣哄帶閹芥粓寮幖浣哥煑闁逞屽墴濮婅櫣鎷犻垾铏亶濡炪値鍘奸悧蹇曞垝鐠囨祴妲堥柕蹇曞Х椤旀帡姊洪幆褎绂嬮柛瀣嚇椤㈡瑩骞掑Δ浣叉嫽婵炶揪绲介幉锟犲箚閸儲鐓涢柛顐亜婢ф挳鏌熼姘伃妞ゃ垺绋戦~婵嬫偂鎼淬埄鍚欓梻鍌欑濠€閬嶆惞鎼淬劌绐楅柡宥冨妼閸旀棃姊婚崒娆戠獢婵炰匠鍥佸洭顢橀姀鐘碉紵闂佺懓澧庨悺鏃堝极婵犲洦鐓欓柣鎴烇供濞堟洟鏌i幘璺烘灈闁哄矉缍佸顒勫箰鎼淬垹鏋戦梻浣规た閸樺ジ顢栭崨绮光偓锕傚锤濡や礁浠梺缁橆殔閻楁粌螞閿曞倹鍊甸悷娆忓缁€鍐煕閵娿儲鍋ラ柣娑卞枛椤粓鍩€椤掑嫬绠犳繝濠傜墛椤ュ牊绻涢幋鐑嗙劷闁告繂楠搁埞鎴︽偐閸偅姣勬繝鐢靛亹閸嬫挸鈹戦悙鏉垮皟闁搞儴鍩栭弲鐐烘⒑缁洖澧茬紒瀣灩婢规洘绻濆顓犲帾婵犵數鍋熼崑鎾斥枍閸℃稒鐓冮梺鍨儏濞搭噣鏌$仦鍓ф创妞ゃ垺娲熸俊鍫曞川椤旈敮鍋撴繝姘拺闁硅偐鍋涙俊铏圭磼閼搁潧鍝虹€殿喖顭峰鎾晬閸曨厽婢戦梻浣告惈濞层劑宕愰敐澶娢ㄩ柍鍝勫€婚崢閬嶆⒑閹稿孩顥嗘い鏇嗗洨宓佹俊銈呮噺閻撴洟鐓崶銊︹拻闁活厼锕ラ妵鍕敂閸曨偅娈堕梺閫炲苯澧剧紓宥呮缁傚秴鈹戠€n亞顔夐梺鎸庣箓濞诧箓宕戦弽顓熺叆闁哄洨鍋涢埀顒€缍婇崺娑㈠箳閹炽劌缍婇弫鎰板醇濠㈩剚鎹囬弻鏇㈠幢濡も偓閺嗭綁鏌″畝瀣М妤犵偞甯¢幃娆撴偨閸偅顔撻梺璇叉唉椤煤濡吋宕查柛顐g箥閸ゆ洟鏌涙繝鍕珡婵′勘鍔戝娲箹閻愭祴鍋撻弽顓溾偓鍐╃節閸パ嗘憰濠电偞鍨崹褰掑础閹惰姤鐓忓┑鐐茬仢閸旀鏌涚€n偅宕岄柟顔规櫇缁辨帒螣鏉炴壆鐩庨梻鍌欑劍閸庡磭鎹㈤幇顒婅€块梺顒€绉甸弲顒佺節婵犲倸鏆婇柡鈧禒瀣厓闁芥ê顦伴ˉ婊堟煟韫囧鍔ら柍褜鍓濋~澶娒洪幋鐘茬筏濠电姵鑹炬闂佽澹嗘晶妤呭磻閸曨垱鐓曢煫鍥ㄦ尵濮g偤鏌熷畡閭︾吋婵﹨娅g划娆撳箰鎼淬垺瀚抽梻浣哄帶缂嶅﹦绮婚弽顓炴槬闁逞屽墯閵囧嫰骞掗幋婵愪紝濠碘槅鍋呴崹鍦閹烘鏁婇柤娴嬫櫅椤も偓缂傚倷鐒﹂〃鍫ュ窗閺嶎厼鏄ラ柍褜鍓氶妵鍕箳閹存繍浼€閻庤鎸风粈渚€鈥﹂崸妤佸殝闂傚牊绋戦~宥夋⒑閸濆嫭鍣洪柟顔煎€垮濠氭晲閸涘倻鍠栧畷褰掝敊閻愵剦鍤勫┑锛勫亼閸婃牠寮婚妸銉冩椽顢橀悜鍡樼稁闂佹儳绻掗幊鎾垛偓鍨叀閺岋繝宕堕埡浣风捕闂佸啿鍢查ˇ杈╂閹惧瓨濯撮柛鎾村絻閸撻亶姊洪幖鐐插闁轰礁顭烽崹楣冨籍閸繄顦ㄩ梺鍐叉惈閸犳艾霉閸曨垱鐓熼幖鎼灣缁夌敻鏌涚€n亝顥㈢€规洏鍨介弻鍡楊吋閸″繑瀚奸梺鑽ゅ枑閻熴儳鈧凹鍘惧▎銏ゅ蓟閵夛妇鍘卞┑顔斤公缁茶姤绂嶉崜褏纾介柛灞剧懇濡剧兘鏌涢弬璺ㄧ闁伙絿鍏橀幃浠嬪垂椤愵偅缍楅梻浣告贡閸庛倝銆冮崨顔煎姅闂傚倷鐒︾€笛呮崲閸岀偛绠犻幖娣灪閸欏繘鏌ㄩ弴妤€浜鹃梺瀹狀潐閸ㄥ潡銆佸▎鎴炲厹鐎瑰嫰顣︾槐锝嗕繆閻愵亜鈧倝宕㈡總绋垮簥闁哄被鍎查崑鈺呮煟閹达絾顥夌紒鐘冲▕閺岀喖骞栭鐐茬闂佺绉瑰褔鈥旈崘顔嘉ч柛鈩冾殘娴煎洤鈹戦埥鍡椾簻閻庢凹鍘剧划瀣吋閸℃劕浜濋梺鍛婂姀閺呮繈宕㈡禒瀣拺缁绢厼鎳忚ぐ褏绱掗幓鎺嗗亾閻曚焦姣愰梻鍌氬€烽悞锕傚箖閸洖纾归柡鍥╁Л閸嬫挸顫濋銏犵ギ閻庢鍠涢褔鍩ユ径鎰潊闁绘ɑ顔栭崯瀣⒒娴h棄浜归柍宄扮墦瀹曟粓鏁冮埀顒€宓勫銈嗘磵閸嬫挻鎱ㄦ繝鍐┿仢妤犵偞鐗犻幃娆撳箵閹烘繄鈧绱撻崒娆愮グ妞ゆ泦鍥х柈閻庢稒眉缁诲棝鏌i姀銏╃劸缂佲偓鐎n偁浜滈柡宥冨姀婢规﹢鏌涢悙顏勫妞ゎ亜鍟存俊鍫曞幢濡も偓琚濇繝鐢靛Л閹冲洭宕戦幘鍓佺=濞撴艾娲ら弸娑橆熆瑜嶅ù宄拔i幇鏉跨閻庢稒锚椤庢捇姊洪崷顓犲笡閻㈩垰锕ョ粩鐔煎即閻愨晜鏂€闂佺粯锕╅崰鏍倶闁秵鐓曢柍鍝勫€绘晶鐢碘偓瑙勬礃缁诲牆顕f禒瀣垫晣闁绘棁娓圭花鐢告⒒娓氣偓濞佳囁囬锕€鐤炬繝濠傜墛閸嬪倹绻涢幋娆忕仾闁绘挻娲熼弻鏇熷緞閸繄浠惧┑鐐叉噹閹冲酣婀侀梺缁樏壕顓㈡儗閹烘鐓涢悘鐐垫櫕鍟稿銇卞倻绐旈柡灞剧洴楠炴鈧潧鎲¢崳鏉课旈悩闈涗沪妞ゃ劌鎳橀垾锕傚Ω閳轰礁绐涘銈嗘尵閸嬬喐绂嶆导瀛樷拻濞达絿顭堥ˉ蹇涙煕鐎b晝绐旂€规洘娲熼弻鍡楊吋閸℃瑥甯掗梻浣规偠閸庢椽宕滃鑸靛亗闁绘柨鍚嬮悡娑㈡煕閹扳晛濡藉璺哄閵囧嫯绠涢弴鐐愶綁鏌曢崶褍顏€殿噮鍣i崺鈧い鎺嗗亾閻撱倝鏌i弬娆炬疇婵炲吋鐗犻弻褑绠涢弴鐔锋畬闁诲骸鐏氶悡锟犲蓟閿熺姴鐐婇柍杞版缁爼姊洪崘鎻掓Щ妞わ妇鏁诲濠氭晝閸屾氨顦ㄥ銈嗘⒒缁垶宕板鑸碘拺閻犲洠鈧櫕鐏嶅銈庡幖閻楀繒鍒掔拠娴嬫闁靛繆鍓濆▍婊堟⒑閸涘﹣绶遍柛姗€绠栭、娆撳箳閺冨倻锛濋梺绋挎湰閻燂妇绮婇弶娆炬富闁哄鍨堕幉鎼佹煛娓氬洤娅嶉柡浣规崌閹晠宕f径瀣撴岸姊绘笟鈧埀顒傚仜閼活垱鏅堕鐐寸厪闁搞儜鍐句純濡ょ姷鍋炵敮鎺楊敇婵傜鐐婇柤鍛婃櫕濠婂懐纾介柛灞剧懅椤︼箑顭胯闁帮絽鐣烽幋锕€围濠㈣泛锕ㄩ幗鏇㈡⒑缂佹ɑ鐓ラ柛姘儔閹偞绂掔€n偆鍙嗛梺鍝勬处椤ㄥ懏绂嶉幆顬棃鎮╅棃娑楁勃闂佹寧娲忛崹钘夘嚕鐠囨祴妲堟慨妤€妫欏娲⒑缁洖澧叉繛鑼枛瀹曟垵螖閳ь剟鍩為幋锔绘晩缁绢參鏀遍弫鎯р攽閿涘嫬浠╂俊顐㈠閹儳鐣¢柇锔惧弳闂佸壊鍋呯换鍕敊瀹€鍕拺闁荤喓澧楅幆鍫㈢磼婢跺﹦鍩g€规洘鐟╁畷鐑筋敇閻樼绱抽梻浣侯焾閺堫剟鎮烽敂鍓х焾闁绘鐗勬禍婊堟煛閸パ勵棞婵炲眰鍊濋幃鍧楊敊閸撗勶紡闂佽鍨庣仦钘夊闂備焦瀵х粙鎴﹀磹閸噮娼栫紓浣股戞刊鎾煣韫囨洘鍤€缂佹せ鈧剚娓婚柕鍫濋楠炴牗绻涘顔煎箹妞ゆ洩缍侀、鏇㈡晝閳ь剚瀵奸悩缁樼厪濠㈣泛鐗嗛崝瀛樹繆椤愶絿鐭嬬紒缁樼箞濡啫鈽夊Ο宄颁壕闁归棿绀佺粻鐔兼煥閻斿搫校闁稿鍊块弻娑㈠箛闂堟稒鐏嶉梺鎶芥敱閸ㄥ墎鎹㈠☉銏犲耿婵☆垰鎼慨銏ゆ⒑鐠囪尙绠冲┑顔芥尦濠€浣糕攽閻樿宸ラ柣妤€绻橀幃楣冩倻濡寮挎繝鐢靛Т閹冲繘顢旈悩鐢电<妞ゆ梻鏅幊鍐煃鐠囨煡鍙勬鐐叉椤︽彃顭块悷閭︽█婵﹦绮幏鍛村川婵犲懐顢呴梻浣侯攰濞呮洟骞愰崫銉ュ疾闂備線娼ч悧鍡浡ㄩ埀顒傜磽瀹ュ棛澧甸柣鎿冨亰瀹曞爼濡搁敂缁㈡Ф缂備胶鍋撻崕鎶藉触鐎n偆鈹嶅┑鐘叉祩閺佸秵绻濋棃娑欘棛婵顨婂铏规兜閸涱喚褰х紓浣筋嚙閻楀棝锝炶箛鎾佹椽顢旈崨顖氬Х闂備胶绮崝妯间焊椤忓棌鍋撳顓熺凡妞ゎ叀鍎婚ˇ鎶芥煙閸涘﹤鈻曠€殿喛顕ч埥澶愬閻橀潧骞嬮梻浣筋嚃閸ㄥ酣宕掑鍏碱棥婵犵數濮烽。顔炬閺囥垹纾婚柟杈剧畱绾惧綊鏌″搴′簼闁哄棙绮撻弻鐔兼倻濮楀棙鐣剁紒鐐劤缂嶅﹪寮诲☉妯锋婵鐗嗘慨娑橆渻閵堝倹娅婇柡鈧潏鈺傚床婵犻潧娲ㄧ弧鈧梺绋挎湰缁矂路閳ь剟姊绘担铏瑰笡闁瑰摜鍋撻幈銊╂偨閸偄搴婂┑鐐村灟閸ㄦ椽宕甸幋婢盯鎮ч崼銏㈢暤濠电偛鐗滈崣鍐潖閾忚瀚氶柡灞诲劤瀹曨亞绱撴担铏瑰笡缂佽鐗嗛锝嗙節濮橆厽娅㈤梺缁樕戣ぐ鍐玻濞戞﹩娓婚柕鍫濇鐏忛潧鈹戦鑺ュ唉闁诡噯绻濋幃銏ゆ嚃閻戞ɑ顥堥柟顔规櫊濡啫鈽夊Δ浣稿闂傚倷鐒︾€笛兠鸿箛娑樺瀭濞寸姴顑呰繚婵炶揪绲跨涵鍫曞几鎼淬劍鐓欓柣鎰靛墯缂嶆垵霉閻樺眰鍋㈤柡宀嬬秬缁犳盯寮撮悙鏉挎憢婵犵妲呴崑鍕偓姘煎枤閸掓帞绱掑Ο渚殼闁诲孩绋掕彜闁归绮换娑欐綇閸撗勫仹闂佺儵鍓濆Λ鍐ㄧ暦闂堟稈鏋庨柟瀵稿Х閿涙粎绱撻崒娆戝妽闁挎碍绻涢幖顓炴灓闁逞屽墲椤煤濮椻偓瀹曞綊宕稿Δ鈧粻鏍煃閸濆嫭鍣洪柟顖滃仦閵囧嫰骞囬埡浣轰患婵炲鍘ч柊锝咁潖缂佹鐟归柍褜鍓欓…鍥樄闁诡啫鍥у耿婵炴垶鐟﹀▍鏍⒑缁洖澧查柨姘辩磼閸撲礁浠滈柍瑙勫灴閹晠宕f径瀣棷闂備礁鎲¢悷銉ノ涘┑鍡╂綎婵炲樊浜滃婵嗏攽閻樻彃鏆熼柨娑欐礋濮婃椽宕崟顒€娅ら梺鑽ゅ暀閸ャ劌娈熼柡澶婄墑閸斿海寮ч埀顒€鈹戦鏂や緵闁告ɑ鎮傞獮蹇撁洪鍛嫼闂佺厧顫曢崐鏇㈠几閹寸偟绡€闁靛繆妲勯懓鍧楁煕閳哄倻娲寸€殿噮鍣e畷濂告偄閸濆嫬绠為梻浣筋嚙閸戠晫寰婃繝姘閻忕偟鍋撻崣蹇涙煕鐏炴儳顥氶柛瀣尵閹叉挳宕熼鍌ゆО闂備焦鎮堕崝宥団偓绗涘洤绠為柕濞炬櫅閻掑灚銇勯幒鎴濐仾闁绘挸鍟撮弻娑㈠Ω閿旈敮濮囧┑鐐叉噹閹冲酣婀佸┑鐘诧工閻楀繘鎮惧ú顏呯厵妞ゆ梻鍘уΣ濠氭煃鐠囧弶鍞夌紒鐘崇洴楠炴瑩宕樿濡垳绱撻崒娆戭槮濠⒀傜矙瀹曟垿骞樼拠鑼暫闂佺鐬奸崑娑㈡嫅閻斿摜绠鹃柟瀛樼懃閻忊晝绱掗銏⑿ч柡灞界Х椤т線鏌涢幘璺烘瀻闁伙絿鏌夐妵鎰板箳閹达附鏆呮繝寰锋澘鈧劙宕戦幘瀛樹氦婵犻潧娲ㄧ粻楣冨级閸繂鈷旈柟顔垮亹閻ヮ亪顢橀埄鍐€愰柛妤呬憾閺屾盯顢曢妶鍛€鹃梺鍛婄懃缁绘垶绌辨繝鍥ч柛灞剧煯婢规洘绻濈喊妯活潑闁稿鎳橀幃鐑藉煛娴g儤娈鹃梺鐟板⒔缁垶藟閸喓绠鹃柟杈剧秮閸濇椽鎮楅棃娑氱劯婵﹥妞藉Λ鍐ㄢ槈濮橆剦鏆繝纰樻閸嬪懘銆冩繝鍥х畺闁绘劖鐣崑鍛存煕閹般劍娅囬柛姗€浜堕弻锝嗘償椤栨粎校婵炲瓨绮嶇换鍫濈暦鐎圭姰浜归柟鐑樻尭娴滄姊洪棃娑氬妞わ缚鍗抽幃鈥斥槈濮橈絽浜炬鐐茬仢閸旀艾螖閻樿櫕鍊愰柣娑卞櫍瀵粙顢橀悢鍝勫箺闂備浇顫夊畷姗€骞撻鍫熷殌闁秆勵殕閻撴稓鈧厜鍋撻柍褜鍓熷畷浼村箛椤掑鍔烽棅顐㈡处閺岋綁宕戦崨瀛樼厱闁硅埇鍔嶅▍鎾绘煃瑜滈崜娆戠矓閻熼偊娼栨繛宸簻娴肩娀鏌涢弴銊ュ妞ゅ孩鐩娲川婵犲啫鏆楅梺鍝ュУ閻楁洟顢氶敐鍥ㄥ珰婵炴潙顑嗛~宥夋⒑闂堟稓绠冲┑顔芥綑閻g敻宕卞☉娆屾嫼闂傚倸鐗婃笟妤呮倿妤e啯鐓曢幖娣灩椤ュ鏌ゅú顏冩喚闁诡喕绮欏畷銊︾箾閻愵剙顏归梻鍌欑閹诧紕鎹㈤崒婧惧亾濮橆剙妲婚摶锝夋煕椤愮姴鍔滈柣鎾存礃缁绘盯宕卞Δ鍐唶闂佸搫妫欓悷锕傚Φ閸曨垼鏁冮柕蹇嬪灮椤旀帡姊洪崷顓炲付缂傚秴锕ら悾鐑芥倻缁涘鏅i梺缁橈耿濞佳囩嵁閸℃稒鈷掗柛灞剧懅椤︼箓鏌熺拠褏绡€闁诡啫鍥х闁挎洍鍋撶紒鈧崼鐔虹瘈闂傚牊渚楅崕蹇涙煛鐎b晝顦﹂摶鏍煥濠靛棙鍣归柡鍡欏仱閺屽秹鏌ㄧ€n亞浠肩紓浣介哺閹稿骞忛崨瀛樺剬闂傗偓閹邦喛绻戝┑鐘垫暩閸嬫盯鎮ф繝鍋搫顭ㄩ崨顕呮綗闂佸湱鍎ら〃蹇涘极婵犲洦鐓犻柟顓熷笒閸旀氨鐥弶璺ㄐ㈡い顏勫暣婵″爼宕卞Ο灏栨晬缂傚倸鍊哥粔宕囨濮樿泛违濞撴埃鍋撶€殿喗鎸虫慨鈧柍鈺佸暞閻濇洜绱撻崒姘偓鐑芥倿閿曚焦鎳屾繝鐢靛仜閹冲繐螞閸愵煈娼栫紓浣诡焽閻熷綊鏌嶈閸撶喖宕洪埀顒併亜閹烘垵鈧憡绂掑鍫熺厾婵炶尪顕ч悘锟犳煛閸涱厾鍩f鐐达耿椤㈡瑩鎮剧仦钘夌濠电姷鏁搁崑鐐哄垂闂堟稓鏆︽い鎺嗗亾闁宠绉撮濂稿幢閳哄偆鍟嶉梻浣虹帛閸旀牕顭囧▎寰濆綊顢欑粵瀣啍闂佺粯鍔橀婊堢叕椤掑嫭鐓欓柣鎾虫捣缁夌儤銇勯姀鈩冪闁轰焦鍔栭幆鏃堝閳哄偆妫冮梻鍌氬€搁崐鐑芥嚄閸撲焦鍏滈柛顐f礀濡ê銆掑锝呬壕閻庤娲橀崹鍧楃嵁濮椻偓楠炲洦鎷呴悷鎵В闂傚倷绶氬褔鎮ч崱妞㈡稑螖閸愵亞鐣堕梺鍦劋椤ㄥ棝鎮¢弴鐐╂斀闁绘ɑ褰冮弳鐐烘煕婵犲啫濮嶉柟绋匡躬閹垽宕ㄦ繝鍌氫紟婵犵妲呴崹浼存倶濠靛鍋傞柟鎵閻撶喖鏌熼幆褏鎽犵紒鈧€n喗鐓涢悘鐐额嚙婵倻鈧鍣崳锝呯暦閸撲焦宕夐柣鎴烇供閸炴彃鈹戞幊閸婃鎱ㄩ悜钘夌;闁绘劖浜介埀顒€鍟换婵嬪炊瑜戦幗鏇炩攽閻愭潙鐏熼柛銊︽そ瀹曟垿骞囬悧鍫㈠幈闂佸綊鍋婇崢鑲╁緤缂佹ǜ浜滄い鎰剁到濞搭喗鎱ㄦ繝鍐┿仢鐎规洦鍋婂畷鐔碱敇閻樻彃蝎缂傚倸鍊烽悞锕併亹閸愵喖鐒垫い鎺戝€搁弸鏂棵瑰鍕噰婵﹦绮粭鐔煎焵椤掑嫬鐒垫い鎺戝€告禒婊堟煠濞茶鐏¢柡鍛埣楠炴﹢顢欓悾灞藉箥婵$偑鍊栭弻锝夊礉鐏炵煫娲Χ婢跺苯绁﹂梺闈涢獜缁辨洜绮绘ィ鍐╃厱闁斥晛鍘鹃鍫熷€堕柍鍝勬噺閻撶喖鏌ㄥ┑鍡樺櫧闁糕晪绲鹃幈銊︾節閸愨斂浠㈤悗瑙勬礈閸忔﹢銆佸鈧幃娆撳箵閹烘繄鈧崬鈹戦敍鍕杭闁稿﹥鍨垮畷婵堜沪鏉炴寧绋戦埞鎴犫偓锝庝簽閻f椽姊虹捄銊ユ灁濠殿喗鎸冲畷锟犲箮閼恒儳鍘介梺鍝勫暙閸嬪棝鎮為崜褉鍋撳▓鍨灈闁诲繑绻堥崺鐐哄箣閿旂粯鏅╃紓浣圭☉椤戝棝鎮剧捄琛℃斀闁宠棄妫楁禍婵囥亜閵娿儲顥㈢€殿喗鐓″畷濂稿即閻愭鍚嬫俊鐐€栭弻銊︽櫠娴犲鏅繝濠傚缁♀偓闂侀潧楠忕徊鍓ф兜閻愵兙浜滈柟瀛樼箖椤ャ垹鈹戦敓鐘虫锭闁宠鍨归埀顒婄秵閸嬪棝宕㈤幖浣瑰€甸柛蹇擃槸娴滈箖鏌f惔顖滅У闁告挻鐩弫宥夋偄閸濄儳顔曢柣搴f暩椤牓顢撻幘鍓佺<闁绘娅曞畷灞绢殽閻愭彃鏆g€规洘绮忛ˇ杈ㄧ箾瀹€濠佺凹缂佺粯绻堝Λ鍐ㄢ槈濮楀棔鎮i梻浣告啞濮婂湱鍒掗幘璇茶摕闁哄洢鍨归悙濠勬喐瀹ュ鏁傛い鎺嶉檷娴滄粓鏌ㄩ弴姘樂闁告凹鍋嗙槐鎺撴綇閵娿儲璇為梺纭呮珪缁挸螞閸愩劉妲堟俊顖滅帛閸ゅ牓姊虹拠鎻掝劉妞ゆ梹鐗犲畷鏉库槈閵忊晜鏅悷婊勬瀹曟椽濡烽敃鈧欢鐐烘煙闁箑澧绘繛鐓庯躬濮婅櫣绱掑Ο鏇熷灴椤㈡瑩寮介鐐垫焾闁诲函缍嗛崰妤呭煕閹达附鐓犲┑顔藉姇閳ь剚娲熼悗閿嬬節閻㈤潧浠滈柟閿嬪灩缁辩偞鎷呴崫銉︽闂佸搫娲㈤崹鐟版纯濠电姰鍨煎▔娑㈩敄閸涙潙鐒垫い鎺嗗亾闁绘牕銈稿璇测槈閵忊晜鏅濋梺缁樕戣ぐ鍐╂叏閺囥垺鈷戠紒瀣皡瀹搞儵鏌h箛鏃€鐨戦柟骞垮灩閳藉濮€閻樿鏁规繝鐢靛█濞佳囨偋閸涘瓨鎯為幖娣妽閳锋垿鏌涘┑鍡楊伌闁稿孩鍔楃槐鎺斺偓锝庡亜濞搭喖鈹戦敍鍕毈鐎规洜鍠栭、娑㈡晲閸℃ɑ鐝濋梻鍌欒兌缁垵鎽悷婊勬緲閸熸挳鎮伴閿亾閿濆骸鏋熼柛濠傜仛缁绘盯宕煎┑鍫滆檸濠电偛鎳忛敃銏ゅ蓟濞戞埃鍋撻敐搴濇倣闂婎剦鍓熼弻锝呪槈閸楃偞鐝濋悗瑙勬礀閻栧ジ銆佸Δ鍛劦妞ゆ帒鍊诲Λ顖滄喐閺冨牆钃熸繛鎴旀噰閳ь剨绠撻獮瀣攽閸モ晙绮氶梻鍌欑窔閳ь剛鍋涢懟顖涙櫠椤曗偓閺岋綀绠涢弮鍌滅杽闂佺硶鏅濋崑銈夌嵁鐎n喗鏅濋柍褜鍓熼幃锟犳晸閻樺磭鍘遍梺鏂ユ櫅閸犳艾鈻撳Ο濂藉綊鎮╅锝嗙彋濠殿喖锕ュ钘夌暦閻戠瓔鏁囨繛鎴炵懃閻濋亶姊绘担渚劸妞ゆ垵鎳橀獮濠呯疀閺囩姷鐓旈柡澶婄墑閸斿海寮ч埀顒勬⒑閹肩偛鍔€闁告粈绀侀弫鍫曟⒒閸屾瑧顦﹂柛姘儐缁傚秵绂掔€n亞锛熷銈嗘磵閸嬫挻顨ラ悙鑼缂佽鲸甯掕灒闁兼祴鏅╅崯搴ㄦ⒒娴e憡璐¢柛瀣尭椤洤鈻庨幘鏉戔偓璺ㄦ喐閻楀牆绗氶柣鎾存礋閹鏁愭惔鈥茬凹闁诲繐绻戞竟鍡欐閹烘梻纾兼俊顖氱毞婵洭姊洪悷鏉挎Щ闁硅櫕锚閻e嘲顫滈埀顒€鐣烽敐鍡楃窞濠电姴鍠氭禒顓㈡⒑鐠囧弶鍞夋い顐㈩槸鐓ゆ慨妞诲亾闁诡噯绻濋弫鎾绘偐閼艰埖鎲伴梻浣虹帛閺屻劑宕ョ€n喖纾圭紓浣姑肩换鍡樸亜閺嶃劎绠ラ柛銈嗙懇濮婄粯寰勬繝鍕懷勬叏婵犲啯銇濈€规洏鍔嶇换婵嬪礋椤掆偓濞呮垹绱撻崒娆掑厡缂侇噮鍨堕弫鍐閻欌偓閸ゆ洖鈹戦悩瀹犲闁绘帗妞介弻娑㈠箛閳轰礁顬嬬紓浣瑰姉閸嬨倝寮婚敐鍡樺劅妞ゆ牗绮庢牎濠电偛鐡ㄧ划宥囨崲閸儱绠氬ù锝堫潐閸庣喖鏌曟繝蹇氬悅闁归攱妞藉娲閳轰胶妲i梺鍛娒妶绋跨暦濠靛牃鍋撻敐搴′簴濞存粍绮撻弻鏇熺箾閸喖濮曢梺鎼炲€曞ú顓㈠蓟閿涘嫪娌紒娑橆儏閸撳爼鎮楃憴鍕闁绘牕銈搁妴浣肝旀担鐟邦€撻梺鍛婄箓鐎氼剚淇婇崶銊х瘈闁汇垽娼цⅷ闂佹悶鍔岄妶绋跨暦濞差亜鍐€妞ゆ劑鍊楅悡鎾绘⒑閸濆嫮鈻夐柛妯垮亹閹叉挳鏁冮崒娑氬幈閻庡厜鍋撻柍褜鍓熷畷鎴︽倷閻戞ê浜楀┑鐐叉閹稿鍩涢幋锔界厱妞ゎ厽鍨靛▍姗€鏌涙惔銏犲闁哄本娲熷畷鍫曞Ω瑜忛悾娲⒑闁稓鈹掗柛鏂跨Ф閹广垹鈹戠€n亞顦ㄩ梺宕囨嚀閵囨﹢鎼规惔銊︾厽閹兼番鍊ゅ鎰箾閹绘帞绠荤€规洘绻傞濂稿炊閵娿儱绨ユ繝鐢靛█濞佳囶敄閸涱垳鐭嗛悗锝庡枟閻撳繐鈹戦悩鑼闁伙附绮嶇换娑㈠礂閸忕⒈妫冨┑顔硷工椤嘲鐣烽幒鎴旀瀻闁瑰瓨绻傞‖澶愭⒑鐠囧弶鎹i柣鐔稿▕瀹曟鎮╅搹顐犱虎闂佺硶鏅换婵嗙暦濮椻偓椤㈡棃宕橀鍡樺枓闂傚倸鍊峰ù鍥綖婢跺﹦鏆︽俊顖濇閺嗭箓姊婚崼鐔恒€掗柡鍡愬€曢湁闁挎繂娲ㄩ妴濠囨煛閳ь剚绂掔€n偆鍘藉┑鈽嗗灠閹碱偆鐥閺岀喖宕楅悡搴☆潕缂備浇椴哥敮锟犲春閳ь剚銇勯幒鎴濐仼缂佲偓閸愵喗鐓冮柣鐔诲焽娴犳帞绱掗妸銉吋婵﹥妞藉畷顐﹀礋椤愶絾顔勯梻浣侯焾閿曪箓骞婇幘璇茬厺鐎广儱顦崡鎶芥煏韫囥儳纾块柛妯哄船閳规垿顢欐慨鎰捕闂佺顑嗛幐鎼佹箒濠电姴锕ゅΛ娆戞兜閻愵兙浜滄い鎰╁灮缁犲鏌熼悡搴gШ鐎规洜鍏橀、姗€鎮崨顖氱哎婵犵數濮烽。钘壩i崨鏉戝瀭闂傚牊绋撻弳锕傛煟閵忕姵鍟為柡鍜佸墯缁绘盯骞嬮悙瀵告缂佺偓宕樺Λ鍕箒闂佹寧绻傚Λ妤冨緤鐠囪鐟邦煥閸涱厺澹曠紓浣虹帛缁嬫帒顭囪箛娑樼鐟滃秹宕虹仦瑙f斀闁绘﹩鍋勬禍楣冩⒒娓氬洤澧紒澶嬬叀閸┾偓妞ゆ巻鍋撻柟铏耿閻涱噣骞樼拠鑼唹濠德板€愰崑鎾剁磽瀹ュ拑韬鐐插暣閸╁嫰宕橀埡浣稿Τ闂備焦瀵х换鍌毼涘▎鎾崇獥闁哄稁鍘介埛鎺懨归敐鍫燁仩閻㈩垱鐩弻鐔虹矙濞嗗墽鍚嬮梺璇″枤閸忔﹢寮崘顔肩<婵絿銆嬬粻鎾诲蓟濞戙垹鍗抽柕濞垮劤娴犫晝绱撴笟鍥т簻缂佸缍婂璇测槈閵忕姈銊︺亜閺冣偓閸庡磭鏁妷銉㈡斀闁宠棄妫楁禍婊堟倵濮橆厽绶叉い顐㈢箰鐓ゆい蹇撳缁愭稒绻濋悽闈浶㈤柛鐔跺嵆瀹曘垺绂掔€n偀鎷虹紓浣割儏鐏忓懘寮ㄩ懡銈囩<閻犲洩灏欐晶鏇熴亜閺囶亞绋荤紒缁樼箓椤繈顢橀悢鍝ュ礁婵犵數濮伴崹鐓庘枖濞戙埄鏁勯柛鈩冦仜閺嬪秵绻濇繝鍌滃妞ゃ儱锕ラ妵鍕箛閳轰胶浠炬繝銏f硾鐎氼厾鎹㈠☉銏犵煑濠㈣泛鐬奸悡澶愭⒑鐠団€崇仧缂佽埖鑹鹃悾鐑芥偂鎼搭喚鍞靛銈呯箰閹冲繘藟閸儲鐓欐い鏃囶潐濞呭﹥淇婇銏犳殭闁宠棄顦灃闁告劏鏅涚粈瀣磽閸屾艾鈧悂宕愭搴g焼濞撴埃鍋撻挊婵囥亜閺嶃劎鐭岀紒鈧繝鍌楁斀闁绘ê寮堕幖鎰交濠靛洨绠鹃弶鍫濆⒔閹偐鐥鐐靛煟鐎殿喖鎲¢幆鏃堝Ω閿旀儳骞嶉梻浣虹帛閸旓箓宕滃杈╃闁瑰鍋熺粻楣冩煕椤愮姴鐏╅柡瀣⊕閹便劍绻濋崘鈹夸虎濠碘槅鍋勯崯顐﹀煡婢跺缍囬柕濞垮灪閻忎線姊婚崒娆戭槮闁硅姤绮嶉幈銊╂偨閸涘﹤浜遍梺缁樏Ο濠囧吹閺囥垺鐓涢悘鐐额嚙閸旀挳鏌℃担鍛婂枠闁哄本娲濈粻娑欑節閸愰敮鍋撻崱娑欑厵鐎瑰嫰鍋婇悡鍏兼叏婵犲懏顏犵紒顔界懇楠炴劖鎯旈姀鈥愁伆闂傚倷鑳堕崢褏绱炴繝鍕笉闁哄稁鍘奸弰銉╂煃瑜滈崜姘跺Φ閸曨垰绠抽柟瀛樼妇閸嬫捇骞栨担绋垮亶闂佸湱铏庨崰妤呮偂濞嗘劑浜滈柡鍐e亾闁稿氦娅曠粋鎺楁焼瀹ュ棛鍘告繛杈剧悼椤牓寮抽敐鍥e亾鐟欏嫭绀冮悽顖涘浮閿濈偛鈹戦崶銊хФ闂佸啿鎼崐褰掓儊閹烘鈷掗柛灞捐壘閳ь剟顥撶划鍫熸媴閸︻厾褰炬繝鐢靛Т濞层倗澹曟繝姘厱婵炴垵宕慨鍛婄箾瀹割喕绨婚柛鎰ㄥ亾婵$偑鍊栭崝鎴﹀春閸曨倠娑橆煥閸啿鎷洪梺闈╁瘜閸欏酣鎮為悙顒傜闁圭虎鍣Λ鎴犫偓娈垮暙閸パ呭姦濡炪倖甯婇懗鍓佸姬閳ь剟姊哄Ч鍥х伈婵炰匠鍐懃闂傚倷鑳堕…鍫ユ晝閵堝洨绀婂┑鐘插€婚弳锕傛煙閹増顥夌€瑰憡绻傞埞鎴︽偐閹绘帩浼€濡炪倖姊瑰ú鐔煎箖濡ゅ懎绀傚璺猴梗婢规洖鈹戦悩鍨毄濠殿喗濞婇幊妤呭醇閺囩偞鐎梺鍝勭▉閸嬪棛澹曢挊澹濆綊鏁愰崟顓犵厯闂佸憡绻冨浠嬪蓟閻旇櫣鐭欐繛鍡楀⒔閸氬螖閻橀潧浠滅紒缁樏悾鐑藉Ω瑜夐崑鎾斥槈濞嗘瑤绶靛┑鈽嗗亜閸燁偊鍩為幋锔藉€烽柡澶嬪灩娴犳悂姊哄ú璇插季闁革綇缍侀獮鍡涘焵椤掍降浜滈煫鍥ㄦ尵婢ф盯鏌嶉柨瀣瑨闂囧鏌ㄥ┑鍡樺闁搞倐鍋撴俊鐐€栧ú妯煎垝鎼达絾顫曢柟鐑樻煛閸嬫捇鏁愭惔鈥茬盎闂佽绻愰悺銊┿€冮妷鈺傚€烽悹鍥囧啩绱i梺鍙ョ串缁蹭粙濡撮幒鎴僵闁绘挸娴锋禒顓犵磽閸屾氨孝閻庢稈鏅濋幑銏犫攽鐎n偄浠洪梻鍌氱墛閸掆偓闁挎繂顦伴悡鐘绘煟閻斿憡绶查柍閿嬫煥椤法鎲撮崟顒傤槹閻庤娲橀〃濠囧箠閺嶎厼鐓涢柛鎰劤閺咁參姊婚崒娆掑厡缁绢厼鐖煎畷婊冣攽鐎n偅娅旀繝鐢靛У椤旀牠宕伴弽顓勫洭鎮界粙鑳憰闂佸搫娲㈤崹褰掓煁閸ヮ剚鐓熼柡鍌涘閹叉悂鏌涢幋鏂哄亾閹颁焦瀵岄梺闈涚墕缁ㄨ偐鑺辨繝姘厱闁绘棃顥撻幗鐘睬庨崶褝韬€规洖銈稿鎾倷閼煎灈鍋撻崹顔规斀闁宠棄妫楅悘鐘绘煟韫囨梻绠栫紒鍌氱Ч瀵粙顢橀悢鍙夊濠电偠鎻紞鈧い顐㈩樀瀹曟垿鎮╃紒妯煎幈闁瑰吋鐣崹濠氭儗閹烘柡鍋撶憴鍕濞存粍绻堥獮蹇涘川閺夋垹顦梺褰掑亰閸犳牠寮稿☉娆愬弿濠电姴鍋嗛悡鑲┾偓瑙勬礃鐢帡鍩㈡惔銊ョ疀闁割煈鍋€閺嬪牏绱撻崒姘偓椋庢濮樿鲸鍏滈柟闂寸缁愭鎱ㄥ鍡楀⒒闁搞倖顨呴埞鎴︽偐閹绘帗娈跺銈傛櫇閸忔﹢骞冨Δ鍛櫜閹肩补鈧尙鐩庢繝鐢靛仜閻楃偟寰婃禒瀣р偓鏃堝礃椤斿槈褔鏌涢埄鍐噧妞ゎ値鍛=濞撴艾娲ら弸娑氱磼婢跺﹦绉洪柕鍡曠窔瀵挳鎮㈡笟顖涚カ闂佽鍑界紞鍡涘磻閸℃稑鍌ㄦい蹇撶墛閳锋垿鏌涢幘鏉戠祷濞存粍绻勭槐鎺旀嫚閹绘帗娈婚悗瑙勬礃婵炲﹪鐛惔銊﹀殟闁靛/鍐ㄧ闂傚倷绶氶埀顒傚仜閼活垱鏅堕婊呯<闁稿本绋戠粭褔鏌嶈閸撱劎绱為崱娑樼;闁糕剝绋戦崒銊╂煢濡警妲撮柡鈧禒瀣厓闁芥ê顦伴ˉ婊堟煟韫囧鍔滅紒缁樼洴瀹曨亪宕橀鍠版粓鎮楀▓鍨灍闁诡喖鍊搁悾宄邦潨閳ь剟鍨鹃敃鍌氱闁绘ê寮堕弳鈺呮⒒娴h棄鍚归柛鐘冲姍閹兘濡疯閸嬫挸顫濋崡鐐插箣闂佽鍠氶崑銈夊箖閹呮殕闁逞屽墰婢规洘绺界粙璺ㄩ獓闂佸壊鍋呯粙鎴炰繆閸忚偐绠鹃柟纰卞幖濞呭秹鏌$仦鍓ф创闁糕晝鍋ら獮鍡氼槺濠㈣娲栭埞鎴︽晬閸曨偂鏉梺绋匡攻閻楁粓寮鐣岀瘈闁告洦鍘鹃悞鍏肩箾鏉堝墽鎮奸柛搴涘€濋、鏇熺鐎n偆鍘介梺褰掑亰閸犳牠宕濈€n喗鐓熼柟鎯ь嚟閹冲洦鎱ㄦ繝鍐┿仢妞ゃ垺锕㈡俊姝岊槾闁哄棛濮磋灃闁绘﹢娼ф禒锕傛煟濡ゅ啫鈻堢€殿喛顕ч濂稿醇椤愶綆鈧洭姊绘担鍛婂暈闁圭顭烽幆鍕敍濮樼厧娈ㄥ銈嗗姧缁茶法寮ч埀顒€鈹戦鏂や緵闁告挻绻堥獮妤呭即閵忊檧鎷洪梻鍌氱墛娓氭鎮炴ィ鍐╃厱閹兼惌鍠栧▍宥団偓娈垮枔閸斿秶绮嬮幒鏂哄亾閿濆骸浜為柛姗€浜跺娲棘閵夛附鐝旈梺鍝ュ枍閸楁娊鐛繝鍥х妞ゆ梻鏅崢鍗炩攽閻樼粯娑ф繛璇х畵婵¢潧鈹戦崶銊ュ伎婵犵數濮撮幊蹇涱敂閻樼數纾兼い鏃傛櫕閹冲啴鏌嶇拠鏌ュ弰妤犵偛妫滈ˇ鎻掝熆閻熼偊妯€婵﹦绮幏鍛村川婵犲懐顢呴梻浣侯攰濞呮洟骞愰崫銉ュ疾婵$偑鍊栭幐鍫曞垂绾懐绠芥繝鐢靛仩閹活亞寰婄捄銊﹀厹閻犺桨缍嶉敐澶婇唶闁靛濡囬崢顏堟椤愩垺澶勬繛鍙夌墪閻☆參姊绘担绋挎倯婵犮垺锕㈤幃妯衡攽鐎n亞鍘撮梺鐟邦嚟閸嬫稓绮婚悩缁樷拺缂佸灏呴弨濠氭煕閺冣偓閻熴儵鎮鹃悜钘夌闁挎洍鍋撶紒鐘哄吹缁辨挻鎷呯拠锛勫姺闂佸憡锕㈠褔鈥旈崘顔嘉ч柛鈩冿供濮婂灝顪冮妶搴′簻妞わ富鍨堕崺銏狀吋閸℃瑧鐦堥梺鎼炲劘閸斿酣宕㈤幖浣瑰€甸柛蹇擃槸娴滈箖鏌f惔顖滅У闁告挻鐩幆渚€宕奸妷锕€鈧敻鎮峰▎蹇擃仾缂佲偓閸愵喗鐓ラ柡鍥悘顏勄庨崶褝宸ユい顐犲灩閻f繃绻濋崘鍐f櫆娣囧﹪鎮欓鍕ㄥ亾瑜忓濠囧箚瑜滃〒璇裁归悩宸剰缂佺姵鐗楁穱濠囧Χ閸涱喖娅ら梺绋款儜缁绘繈寮婚敐鍛傛棃鍩€椤掑嫭鍋嬮柛鈩冪☉濮规煡鏌涢鐘茬伄缁炬崘妫勯湁闁挎繂娲ㄩ幗鍌炴煕閵堝棛鎳囬柡灞剧洴閹垺顦版惔銏″枛濠电儑绲藉ú銈夋晝椤忓牆绠栭柣锝呯灱閻瑩鎮规笟顖滃帥婵¤尪顫夋穱濠囨倷椤忓嫧鍋撻弽顓熷亱婵°倐鍋撴い顐g箞婵℃悂鍩¢崒姘闂備礁鎲″ú锕傚垂闁秴鐓曢柟杈鹃檮閻撴瑩鏌ゅù瀣珔濞寸姵绮撻弻娑㈠棘鐠囨彃濮﹂梺鍝勬湰閻╊垶宕洪敓鐘茬<婵犲﹤鍟犻幏锛勭磽閸屾瑦绁板ù婊庡墴瀹曟垿濡堕崨顖涙婵犻潧鍊婚…鍫濇暜闂備焦瀵у褰掑磿閹剁晫宓佹俊銈呮噺閳锋垿鏌i悢鍛婄凡闁诡喗鍨块弻锝夋晲鎼存繈鍋楅悗瑙勬礀缂嶅﹤鐣峰Δ鍛殐闁冲搫鍟鍕節濞堝灝鏋熼柕鍥ㄧ洴瀹曟垿骞樼紒妯煎幐闁诲繒鍋熼崑鎾剁矆鐎n兘鍋撶憴鍕闁靛牆鎲¢幈銊╁焵椤掑嫭鐓冮柛婵嗗閺嗘瑥鈹戦鐓庢倯濞e洤锕幃娆擃敂閸曘劌浜鹃柕鍫濐槸绾惧鏌涢弴銊ュ箺鐎规洘鐓¢弻鐔兼倻濡儵鎷瑰銈庡亝濞茬喖寮婚悢鍏煎€绘俊顖滃劋椤旀洟姊虹紒妯荤叆闁告艾顑夊畷鐢稿礃椤旂晫鍘撻梺鍛婄箓鐎氼剟鍩€椤掑偆鐒鹃柍缁樻崌閹瑩鎮滃Ο閿嬪闂備胶顭堥張顒勬偡瑜忕划锝夊籍閸喓鍘撻悷婊勭矒瀹曟粌鈽夐姀鐘碉紱濠电偞鍨崹娲吹閹邦厹浜滈柡宥冨妿閳洘绻涢崨顖毿i柕鍥у瀵剙鈻庨悙顒傜◥濠电偛鐡ㄧ划宥囧垝瀹ュ桅闁告洦鍨扮粻濠氭偣妤︽寧銆冩繛宀婁邯濮婃椽宕妷銉愶綁鏌ㄩ弴妯虹伈鐎殿喖顭烽幃銏ゆ惞瑜版巻鏀洪梻渚€娼荤€靛矂宕㈡ィ鍐╁剨闁割偆鍠撶弧鈧紒鍓у鑿ら柛瀣尭閻g兘宕惰閸樹粙鏌f惔銈庢綈婵炲弶顭囬弫顕€骞掑Δ瀣◤濠电娀娼ч鎰板极閸愵喗鐓忛煫鍥э攻濞呭棙銇勯妷顖滅瘈婵﹤顭峰畷鎺戭潩椤戣棄浜鹃柟闂寸绾惧綊鏌熼梻瀵割槮缁炬儳缍婇弻鐔兼⒒鐎电濡介梺绋款儏椤戝懘鍩為幋锔藉亹闁圭粯甯╂导鈧梻浣规た閸樹粙鎮烽埡鍛摕闁绘梻鍘х粈鍫㈡喐韫囨洘鏆滄繛鎴欏灪閻撴洖鈹戦悩鎻掆偓褰掑磻閵夆晜鐓涢悘鐐插⒔閳藉鏌嶇憴鍕伌鐎规洜鍠栭、鏇㈠閻欌偓濞兼洟姊婚崒娆掑厡妞ゎ厼鐗撻、鏍幢濞戞顔囨俊銈忕到閸燁偆绮婚悢鍏肩厵缂備降鍨归弸娑氱磼閳ь剛鈧綆鍋佹禍婊堟煙閻戞ê鐏ュù婊勫缁辨帗顫戦弽褍绫嶅┑顔硷功缁垶骞忛崨顖涘枂闁告洦鍋傞崫妤呮⒒娴e憡鍟為柡灞诲妿閹广垽骞囬弶璺ㄥ幒閻庡箍鍎遍ˇ浼村疾閺屻儲鐓曢柕澶堝灪濞呭洭鏌ㄥ☉娆戠疄婵﹥妞介幃鐑藉级鎼存挻瀵栫紓鍌欑贰閸n噣宕圭捄铏规殾闁硅揪绠戦悡娑㈡煕閹板墎鍒板ù婊堢畺閺屾稖绠涢幙鍐┬︽繛瀛樼矒缁犳牕顫忓ú顏呯劵闁绘劘灏€氭澘顭胯閹告娊寮婚悢纰辨晬婵ê鍟块顓㈡⒑鐎圭媭鍤欓梺甯秮閻涱喖顫滈埀顒€顕i崼鏇炵婵犲﹤鍟褍鈹戦悩鍨毄闁稿鍋ら獮鎰節濮橆剛顦╅悷婊呭鐢帡宕归崒鐐寸厵闁诡垳澧楅ˉ澶愭煕鐏炶濡界紒缁樼洴楠炲鎮欓崹顐㈡珡缂傚倷娴囬褍螞濠靛钃熼柕鍫濇搐閺嬪牓鏌涘Δ鍐ㄤ粶妞ゎ偀鏅犲娲川婵炴帩浜幃娲Ω閳轰胶鐤勯梺闈涱煭婵″洨寮ч埀顒勬⒑閸涘﹣绶遍柛锝庡枟缁傛帡鍩¢崨顔规嫼閻熸粎澧楃敮鈺佄涢幋婵冩斀闁绘劏鏅涙禍鐐繆閵堝洤啸闁稿鍋ら獮鎴﹀炊椤掑倸绁﹂梺鍦劋椤ㄥ懐绮婚敐澶嬬厽闁归偊鍓涙禒娑氭偖閻樼數纾介柛灞捐壘閳ь剚鎮傚畷鎰板箹娴e摜锛欓梺褰掓?缁€浣哄瑜版帗鐓曟繝闈涘閸斻倝鏌i鐔稿磳闁哄备鍓濆鍕偓锝庝簼椤旀洖鈹戦悙鏉戠仸閼裤倝鏌¢埀顒佺鐎n偆鍘遍梺鏂ユ櫅閸熶即骞婇崟顒傜闁割偁鍎抽悾鐑樻叏婵犲啯銇濈€规洦鍋婂畷鐔煎垂椤愬稁浜滈—鍐Χ閸℃顦ㄦ繝鐢靛仜閿曘倝顢氶敐澶樻晪闁逞屽墮閻g兘鎮℃惔妯绘杸闂佺硶鍓濋悷褍鐣烽崫鍕ㄦ斀闁挎稑瀚禍濂告煕婵犲啰澧摶鐐烘煕閹扳晛澹嗘繛鎴炵瀹曞鏌曟繛鍨鐏忓繘姊绘担鍦菇闁搞劌缍婇獮澶愭晸閻樿尙鍘遍梺鍦劋閸ゆ俺銇愰幒鎾存珳闂佸憡渚楅崰鏍汲閸儲鈷戦悹鍥b偓宕囦哗闂佺粯顨呴敃锕傚箲閵忕姭妲堟慨姗嗗亝閸曞啴姊虹粙鎸庢拱婵ǜ鍔嶇€靛ジ宕奸妷锕€鈧敻鎮峰▎蹇擃仾缂佲偓閸儲鐓欓柧蹇e亝鐏忕敻鏌涘▎蹇斿櫣妞ゎ亜鍟存俊鍫曞川椤栨粠鍞堕梻浣烘嚀閸熻法鈧稈鏅濈划瀣吋閸涘倹妫冨畷銊╊敋閸涱噮妫呭┑锛勫亼閸婃牠宕濋幋锕€鍨傞柣鎴灻欢鐐烘煕閺囥劌鐏¢柣鎾寸懇閺屾稑鈽夊鍫熸暰闁诲繐楠忔俊鍥焵椤掍緡鍟忛柛鐘虫崌瀹曟繂顓奸崶鈺冪効闂佸湱鍎ら弻锟犲磻閹剧粯鏅查幖绮光偓鑼晼闂備礁鎲$湁缂侇喗鐟ラ~蹇斻偊鐟併倓姹楅梺鍦劋閸ㄦ娊宕版繝鍥ㄢ拺闁硅偐鍋涙俊娲煕濡や礁鈻曟鐐叉瀹曟﹢顢欓梻瀵哥倞闂備礁鎲″Λ浣肝涢崟顓犵濠电姴娲ょ粻鏍煃閸濆嫭濯奸柡浣革躬閺屻倕霉鐎n偅鐝掔紓浣介哺閻熲晛顫忕紒妯诲闁告稑锕ラ崕鎾绘⒑閸濆嫮澧遍柛鎾跺枛楠炲棝宕熼锝嗘櫖濠殿喗顭囬崢褍鈻撻妸銉富闁靛牆妫楃粭鎺楁煕婵犲倹璐¢柍褜鍓氱喊宥囧枈瀹ュ洦宕叉繛鎴欏灩缁狙囨煙閹碱厼骞栭柛鎾跺缁绘稓鈧稒顭囬惌宀勬煕鐎n偅灏扮紒宀冮哺缁绘繈宕堕‖顑洦鐓曟繛鎴濆船楠炴绻涢崼鐔风祷妞ゎ亜鍟存俊鑸垫償閳ヨ尙鍑规繝鐢靛仩鐏忔瑩宕伴弽褜鍤曞┑鐘崇閸嬪嫰鏌涜箛鏇炲付闁逞屽墰缁垱绌辨繝鍥舵晬婵犲灚鍔曞▓顓犵磼閻愵剚绶茬紒澶婂濡叉劙骞樼€涙ê顎撶紓浣割儐椤戞瑩寮抽姀銈嗏拺缂佸顑欓崕宥夋煕婵犲啰绠為柟顔诲嵆椤㈡岸鍩€椤掆偓椤曪絾绂掔€Q€鍋撻弽顓炍ㄩ柕澶嗘櫅瀵澘顪冮妶鍐ㄧ仾妞ゃ劌锕畷娲焵椤掍降浜滈柟鐑樺灥椤忣亪鏌涙繝鍌涘仴闁哄本绋戦埞鎴﹀幢濡炵粯鐏嗛柣鐔哥矌婢ф鏁Δ鍛;闁归偊鍘规禍婊堟煙閺夊灝顣崇紒瀣煼閺岋絽鈹戦崶顏勵棟闂佸疇顫夐崹鍧椼€佸▎鎴炲厹闂佸灝顑嗛弳鐗堢節绾板纾块柛瀣焽閸掓帒鈻庤箛锝呮婵犵數濮甸懝鎯ь啅濠靛鍊垫繛鎴烆仾椤忓牆鐒垫い鎺戝€搁崢鎾煛鐏炶鈧繈骞婂┑瀣亱闁割偒娼块埀顒佸姇椤啴濡堕崨顔绢洶闂佸憡顭囬弲顐﹀箲閵忕姭鏀介悗锝庝簽閸橀亶姊洪柅鐐茶嫰婢у鈧娲橀敃銏′繆濮濆矈妯勯梺缁樼⊕閹瑰洤顫忕紒妯肩懝闁逞屽墮椤洩顦查悡銈夋煏閸繃绀岄柛瀣尭椤繈顢曢姀鐘点偖闂備線娼уΛ鏃傛濮橆剦鍤曢柟缁㈠枛椤懘鏌e▎灞戒壕濠电偟鍘ч敃顏勵潖濞差亜绀冮柛娆忣槹閸庢捇姊虹粙鍖℃敾闁告梹鐟╁顐﹀礃椤旇偐锛滃┑鐐村灦閼归箖鐛Δ鍛拻濞达絿鐡斿鎰版煕鎼粹€虫毐闁伙絿鍏橀、妤呭礋椤愩倕濮︽俊鐐€栫敮濠囨嚄閼稿灚娅犻柛顭戝亽濞堜粙鏌i幇顖氱毢濠⒀嶇畱閳规垿鍩勯崘鈺佲偓鎰攽閿涘嫬鍘存い銏$懇閹稿﹥寰勭仦鎷樻帡姊婚崒娆愮グ鐎规洖鐏氶幈銊╁级閹炽劍妞介崺鈩冪瑹閸パ勵吙闂備浇顫夐崕鎶筋敋椤撱垺鍋熼柛顐f礃閻撴盯鏌涢妷锝呭姎闁诲浚浜弻锝夊箻鐠虹儤鐏堝Δ鐘靛仦閻楁洝褰佸銈嗗坊閸嬫捇鏌嶈閸忔瑩宕愰弴鈶┾偓锕傚炊椤掆偓缁犳稒銇勯幘璺盒ユい鏃€娲熷娲川婵犲嫭鍣у銈忕細缁瑩骞冮悙瀵割浄閻庯綆鍋嗛崢闈浳旈悩闈涗粶闁诲繑绻堥幃姗€鎳犻钘変壕閻熸瑥瀚粈鍐偨椤栥倗绡€妤犵偛鍟埢搴ㄥ箻閺夋垶顓绘俊鐐€栧濠氬磻閹炬惌娈介柣鎰綑濞搭喗鎱ㄦ繝鍐┿仢闁诡喚鍏樺鍫曞箰鎼粹檧鍋撻鐐粹拺濞村吋鐟х粔闈浢瑰搴濈盎闁伙絽鍢查埞鎴﹀幢濞嗘劖鐣烽梻渚€鈧偛鑻晶浼存煕閹烘挸绗氱紒缁樼箓椤繈顢橀悙鎼悑闂傚倷绶氬褔鎮ч崱娑樼9闁告稑锕﹂々鎻捨旈敐鍛殲闁稿鍓濈换娑㈠幢濡ゅ啰顔囧銈呮禋娴滅偟妲愰幒妤€鐒垫い鎺戝閻掑灚銇勯幒鍡椾壕闂佸疇顫夐崹鍧楀箖濞嗘挻鍤戞い鎺嶇鐎b偓闂傚倷绀侀幉鈥愁潖瑜版帒鍨傞柣銏犲閺佸鏌ㄥ┑鍡╂Ц缂佺媭鍠氱槐鎺戔槈濮楀棗鍓遍梺鍝勬噺缁诲牆顫忓ú顏勭閹艰揪绲块悾闈涒攽閻愯尙婀撮柛鏃€鍨块獮鍡樼瑹閳ь剙鐣锋總绋课ㄩ柨鏃囶潐鐎氬吋绻濆▓鍨灓闁硅櫕鎸哥叅闁靛牆顦伴崐鍫曟煕濞嗗浚妲虹紒鐘冲劤闇夐柨婵嗘噹閺嗛亶鎮楀鐓庢珝闁靛棗鎳橀弻銊р偓锝庡墰閻﹀牊绻濋悽闈浶㈤柛濠冩倐椤㈡棁顦寸紒杈ㄥ笧閹风娀宕f径妯伙紒闂備線娼уú銈団偓姘嵆閻涱噣宕堕鈧粈鍫澝归敐鍥ㄥ殌濞寸姴缍婂缁樻媴閻戞ê娈岄梺鍝ュ枎閻忔繄鍙呴梺鎸庢礀閸婂爼鍩€椤掆偓閸熷瓨淇婇悜钘夌厸闁稿本鍩冮崑鎾绘倻閼恒儳鍘告繝銏f硾椤戝懘鎮橀妷锔轰簻妞ゆ劑鍨昏倴缂備浇椴搁幐濠氬箯閸涘瓨鎯為柣鐔稿椤愯偐绱撻崒娆愮グ妞ゆ泦鍥х9闁秆勵殕閺呮煡鏌i幇顓犮偞闁衡偓娴犲鍊甸柨婵嗘噽娴犳盯鏌¢崨顐㈢伈婵﹨娅g划娆戞崉閵娧冨Ы濠电姷顣介埀顒冩珪婢跺嫮绱掔€n亶妯€闁瑰磭濞€椤㈡宕掑鎰棷闂傚倷鑳堕…鍫ュ嫉椤掑嫭鍤屽Δ锝呭暙閻掑灚銇勯幒宥囧妽闁稿﹥鍔楅埀顒冾潐濞叉﹢宕濆▎鎾崇畺婵犲﹤鐗婇崵宥夋煏婢跺牆鍔楅柛瀣崌瀹曠螖娴e搫寮抽梻浣告惈閸燁偊宕愰崨濠勵洸闁告挆鍛紲闂佺粯锚閸熻法绮缁辨帗娼忛妸锕€纾抽悗瑙勬礃鐢帡鍩㈡惔銊ョ疀妞ゆ柨鎼禒鎺戔攽閿涘嫬浜奸柛濠冪墪閳绘棃鏁冮崒姘鳖槯闂佺粯鍔﹂崜娑㈠煡婢舵劖鐓冮悹鍥ㄧ叀閸欏嫭顨ラ悙鐤殿亪鈥﹂崸妤€绀嬮柛鎾茶兌閺嗐倝姊洪崫鍕拱闁烩晩鍨伴锝夊箻椤斿槈鈺呮煏婢诡垰鍊搁幗瀣⒒閸屾瑧顦﹂柟璇х節瀹曟繆绠涘☉妯硷紱闂佺懓澧界划顖炲煕閹烘垯鈧帒顫濋敐鍛婵犵數鍋橀崠鐘诲幢濡や緡浠╅梻鍌氬€风粈渚€骞夐埄鍐懝婵°倕鎳庨崹鍌炴煕濡ゅ啫鈧偊骞掑Δ鈧悙濠冦亜閹哄秷顔夐柟宄邦煼濮婅櫣绮欓幐搴㈡嫳闂佽崵鍟欓崨顖滃箵闂佸搫鍟犻崑鎾剁磼缂佹鈯曢柟宄版嚇瀹曟﹢骞撻幒鎾充汗婵犵數鍋為崹鍫曗€﹂崒鐐茬睄闁割偅绻傜粣娑橆渻閵堝棙灏靛┑顔炬暬閹偞銈i崘鈹炬嫽婵炶揪绲介幉锛勬嫻閿熺姵鐓i煫鍥ㄦ崌閸欏嫮鈧娲戦崡鍐差嚕娴犲鏁囬柣鏃堫棑瑜板懘姊绘担铏瑰笡闁哄被鍔戝畷銉р偓锝庡枟閸嬪倿鏌曟径娑橆洭缂佲檧鍋撻梻鍌氬€搁悧濠勭矙閹烘鏅€广儱妫旂换鍡涙煙缂佹ê绗氶柛鐔哄仱閺屾洟宕惰椤忣厽銇勯姀鈩冪濠殿喒鍋撻梺鐐藉劥濞呮洟鎮炬繝姘拻濞达絽鎲¢幆鍫ユ煛閸偄澧悡銈嗙節闂堟稓澧㈠☉鎾崇У缁绘盯骞嬮悙鑼姲闂佺顑嗛幑鍥极閹邦厽鍎熸繝闈涚墛閺呯厧鈹戦悙宸殶濠殿噣绠栧畷鎴﹀箛椤旂瓔娼熼梺瑙勫劤閻°劍鍒婇幘顔藉仯闁搞儻绲芥晶鍙夈亜閹捐顏犵紒杈ㄦ尰閹峰懏绂掔€n亝鎳欐繝鐢靛仜瀵墎鍒掔仦钘夌カ闂備礁婀辨晶妤€顭垮Ο鑲╀笉濠电姵纰嶉崐鍨箾閹寸儐浠炬い蹇撶墱閺佷線鏌熼崜褏甯涢柍閿嬪灴閺岀喖顢涢崱妤佸櫧妞ゆ柨锕铏规兜閸涱喚褰ч梺鍦焾婢т粙宕氶幒妤婃晣闁靛繆鍓濆▍鏍⒑閸涘﹥澶勯柛姗€绠栭弫宥呪攽閸モ晝顔曢柡澶婄墕婢т粙骞冩總鍛婄厽闁斥晛鍟ˉ鍫⑩偓瑙勬礋濞佳囧煝鎼淬劌绠婚悗鐢殿焾楠炴绻濆閿嬫緲閳ь剚鎹囬幃鐐烘晝閳ь剟鎮惧畡鎵殕闁告洦鍓涢崢钘夆攽閻愭潙鐏ョ€规洦鍓欓埢宥咁吋閸ワ絽浜鹃悷娆忓缁€鍐煥閺囨ê鐏茬€规洘妞介弫鎾绘偐閼碱剦妲伴梻浣虹帛閸旓箓宕滃☉銏犖фい鎰堕檮閳锋帒霉閿濆洨鎽傞柛銈嗙懇閺屾盯骞嬮悩铏彧缂備浇浜崑銈呯暦閸楃偐妲堟俊顖溿€嬬槐閬嶆⒒娴e憡璐¢柛搴涘€濆畷鐢告晝閳ь剟鍩ユ径鎰潊闁绘ɑ顔栧Σ浼存⒒娓氣偓濞佳団€﹂崼銉ュ瀭婵炲樊浜滃Λ姗€鏌嶈閸撶喎顫忕紒妯诲闁惧繒鎳撶粭锟犳⒑閸涘﹥鈷愰柣妤冨█閵嗕礁鈻庨幘鍐插敤濡炪値鍓﹂崜姘辩矙閹烘绠氶柡鍐ㄧ墛閺呮煡鏌涢妷銏℃珨缂佽鲸濞婂缁樻媴缁嬫妫岄梺绋款儏閹虫劙宕氶幒鏂炬勃闁伙絽鏈▓濂告⒑缁洖澧查柣鐔村灲瀹曟垿骞橀懜闈涙瀭闂佸憡娲﹂崜娑⑺囬纰辨富闁靛牆楠告禍婊勩亜閿曚椒鍚柛鎺撳笧閳ь剨缍嗛崰鏍不閹惰姤鐓涢柛灞剧閹牆霉濠婂牏鐣洪柡灞诲妼閳规垿宕卞▎蹇撴瘓婵犵數鍋涢顓㈠礂濮椻偓瀵鎮㈤崗鐓庢疅闂侀潧顧€婵″洭藝閺夊簱鏀芥い鏃傘€嬮弨缁樹繆閻愯埖顥夐摶鐐烘煕閹扮數鍘戠憸鐗堝笒鍞梺闈涳紡閸愶絽寰嶉梺璇插椤旀牠宕板Δ鍕╀汗闁告劦鍠栭悡鈥愁熆閼搁潧濮囨い顐㈡嚇閺岋絽螣濞茶鏅遍梺琛″亾闁靛ň鏅滈埛鎺懨归敐鍥ㄥ殌闁告柣鍊栫换娑氣偓娑櫭崫铏光偓瑙勬礃閸ㄥ灝鐣烽幒鎴叆闁告洦鍋勭花銉╂⒒娴h櫣銆婇柛鎾寸箚瑜扮姵绻涚€涙鐭嬬紒顔芥崌瀵鍨鹃幇浣告倯闂佸憡鍔戦崝宀勨€栫€n剛纾介柛灞捐壘閳ь剛鎳撻悾婵嬪箹娴f瓕鎽曢悗骞垮劚閻楁粌顬婇妸鈺傗拺缂佸娉曠粻鏌ユ煥閺囨ê鐏╅柣锝囧厴楠炲鏁冮埀顒傜不閼姐倗纾藉ù锝夘€囧璺虹闁惧繐婀辩壕钘壝归敐鍛棌闁稿孩鍔栭妵鍕箣閻愬灚鍣伴悗瑙勬礃濞茬喖鐛崶顒佸亱闁割偁鍨归獮宥夋⒒娴e憡鍟炵紒瀣灴閺佸啴濡烽埡浣猴紮闂佽澹嗘晶妤呮偂閺囥垺鐓冮柛婵嗗閺嗘瑥霉閻樻椽鍝烘い銊e劦閹瑥顔忛鐓庡闂備浇妗ㄧ粈渚€宕幘顔兼槬闁逞屽墯閵囧嫰骞掗幋婵愪紑閻庤鎸风欢姘跺蓟閺囷紕鐤€闁靛/鍜冪吹缂傚倷鑳舵繛鈧紒鐘崇墵瀵鈽夐姀鐘靛姶闂佺绻掓刊顓熺濠靛绠為柕濞炬櫅闁卞洭鏌i弮鍌滅瘈缂併劌顭峰娲传閸曨偅娈滈梺绋款儐閹歌崵鎹㈠☉銏″殤妞ゆ巻鍋撻柡瀣閵囧嫰顢曢姀銏㈩唺缂備浇椴哥敮鎺曠亽闁荤姴娲ゅΟ濠囧焵椤掍焦宕屾慨濠冩そ瀹曘劍绻濋崟銊︻潔闂備焦瀵уú蹇涘磿闂堟稓鏆﹂柡鍥ュ灩缁犲鏌熸0浣哄妽閻庨潧鐭傚娲濞戞艾顣虹紓浣虹帛鐢偛危閹邦厼顕遍悗娑欘焽閸樺崬鈹戞幊閸婃挾绮堟笟鈧崺銏ゅ即閵忥紕鍘梺绯曞墲濞叉粎绮i弮鍌楀亾濞堝灝鏋涢柍褜鍓涢崳銉ノi悜鑺モ拺闁告繂瀚烽崕蹇涙⒑鐢喚绉柟顕嗙節椤㈡洟鏁冮埀顒勬倷婵犲偆娓婚悗锝庝簻椤掋垽鏌涚€f柨娲﹂埛鎴︽煕濞戞﹫鏀婚柍閿嬪浮閺屾稖绠涢弬鍡╀邯閿濈偠绠涢幘浣规そ椤㈡棃宕熼褎袨闂傚倷绀侀幉锟犳偡閵夆敡鍥ㄥ閺夋垹锛熼梺鐟板⒔缁垶鍩涢幋鐘电<閻庯綆浜滈惃鈥愁潡椤愶絽鍝洪柡灞剧洴閸╋繝宕掑鍐f嫛缂傚倷绶¢崰鏍敄閸涙惌鏁囧┑鍌滎焾濡炶棄霉閿濆懏鎯堢€殿喗濞婂缁樻媴缁嬫妫岄梺绋款儏濡繂鐣锋导鏉戠閻犲洦褰冮崑宥夋⒑濮瑰洤鐏╅柟璇х節閹繝鎮㈤悡搴n啇濠电儑缍嗛崜娆撴倶椤曗偓閺屽秹顢涘☉娆戭槹闂佸綊鏀遍崹鍧楀蓟閸℃鍚嬮柛鈩冪懃鐢姊婚崒娆戭槮闁诲繑绻堥、鏍川椤旇棄寮块梺鍓插亖閸ㄨ崵澹曢懖鈺冪=濞达綀顕栭悞鑺ョ箾閹绘帩鍤熼柍褜鍓濋~澶娒鸿箛娑樼闁硅揪璐熼埀顑跨椤粓鍩€椤掑嫬绠栭柕蹇嬪€栭悡銉╂倵閿濆骸鍘搁柟顔肩Ч濮婂宕掑顑藉亾妞嬪海鐭嗗〒姘e亾妤犵偞鐗犻、鏇㈡晝閳ь剛鈧艾顦伴妵鍕箳閹存繍浠鹃梺绋块鐎涒晠濡甸崟顖氬唨妞ゆ劦婢€缁墎绱撴担鍝勑i柣妤冨█瀵顓奸崱妯侯潯闂佺懓鍢查懟顖炲储閿熺姵鈷戦柛婵嗗閿涙梻绱掗悩铏磳鐎殿喛顕ч埥澶愬閻樻牓鍔戦弻鐔衡偓娑櫳戦悡銉ッ瑰鍫㈢暫婵﹨娅e☉鐢稿川椤斿灝鎮呴梻浣告啞椤ㄥ棙绻涙繝鍌ゅ殨濠电姵纰嶉弲鏌ユ煕閳╁厾顏堝礉閸涘瓨鈷戦梻鍫熺〒婢ф洟鎮楀☉鎺撴珖缂佽京鍋ゅ畷鐓庘攽閸愨晜鏉搁梻浣虹帛閸旀牞銇愰崘顏嗘/鐟滄棃寮婚妸銉僵妞ゆ挻绮堢花璇差渻閵堝懐绠伴悗姘煎墴瀵娊鎮欓悽鐢碉紲闂佺鏈粙鎴犵箔瑜旈弻宥堫檨闁告挶鍔庣槐鐐哄幢濡⒈娲稿┑鐘绘涧閺屽牓鏁愭径妯绘櫌闂佸憡娲﹂崗姗€骞忓ú顏呪拻濞撴艾娲ゆ禍鐐烘煕鐎n偆娲撮柟宕囧枛椤㈡稑鈽夊▎鎰娇婵$偑鍊栭悧婊堝磻閻愮儤鍋傞煫鍥ㄧ⊕閻撴洟鏌曟径瀣仴闁哥姵纰嶇€靛ジ宕橀妸搴㈡閹晠妫冨☉妤佸媰闂佹眹鍩勯崹杈╂暜閿熺姰鈧礁顫滈埀顒€鐣峰Δ鍛亗閹艰揪绲块悰顕€姊虹拠鎻掑毐缂佹彃娼¢妴鍌涚鐎n亞锛涢梺瑙勫礃椤曆囧礃閳ь剟姊洪棃娴ゆ盯宕担鍛婃珬闂傚倷娴囬褏鈧稈鏅濈划娆撳箳濡炵儵鍋撻敃鍌氱倞妞ゆ帊绀侀崜褰掓煟鎼搭垳绉甸柛鎾寸〒婢规洟宕楃粭杞扮盎闂佸搫鍟ú銈堫暱闁诲氦顫夊ú鏍儔婵傜鐒垫い鎺嶇贰閸熷繘鏌涢悩宕囧⒌闁炽儻绠撻幃婊堟寠婢跺瞼鏆梻渚€娼х换鍫ュ磹閺囩姷鐭嗛柛宀€鍋為悡鐔兼煙閹咃紞鐎光偓閹间焦鐓曢悗锝庡亝鐏忕數绱掓潏銊ョ瑨閾伙綁鏌涢敂璇插箻闁伙絿鍋撴穱濠囨倷椤忓嫧鍋撻弽顓熷亱婵°倕鍟畷鏌ユ煕閹伴潧娅橀柡浣稿€块弻锝呂熷▎鐐挅閻熸粎澧楃敮妤呭磻閹扮増鐓i煫鍥风到娴滅偟绱掔€n亝鎼愭い顏勫暣婵¤埖鎯斿┑鍫㈡晨闂備礁鎽滈崰搴ㄦ偤閵婏妇鈹嶅┑鐘叉搐闁卞洭鏌¢崶鈺佷粶缂佹劖绋戦—鍐Χ閸℃ǚ鎷婚梺鎯х箰妤犲摜鍙呴柣鐘荤細閵嗏偓闁衡偓娴犲鐓熼柟閭﹀灠閻ㄦ椽鏌熼悾灞叫ョ紒杈ㄥ浮椤㈡瑩骞嗛‖顕嗙悼缁辨帡宕掑姣櫻勩亜閵忊剝顥堢€规洜鍠栧Λ鍐ㄢ槈濞嗘ê鎮梻鍌欐祰瀹曞灚鎱ㄩ弶鎳ㄦ椽鏁傞崜褏鐒鹃梺鍝勵槹閸わ箓鏁愭径濠囧敹闂佺粯妫佸▍锝夘敊閺囥垺鈷戠紒顖涙礀婢ф煡鏌ㄥ鑸电厽闊洤锕ュ▍濠囨煛瀹€瀣М闁轰礁鍟撮崺鈧い鎺戝閸嬪鏌熼悙顒€澧繛鍏肩墵閺屟嗙疀閹剧纭€闂佹椿鍘介悷鈺呭蓟閻旇櫣鐭欓柛顭戝櫘閸斿姊洪崷顓熺効濞存粠鍓涘Σ鎰板箻鐎靛摜鎳濋梺鎼炲劀閸曨厺閭梻鍌欒兌缁垶銆冮崨顖涘床婵☆垵娅i弳锔芥叏濡寧纭剧紒鐘烘珪娣囧﹪濡堕崟顓фМ婵炲濮靛钘夘潖閸濆嫅褔宕惰娴煎嫰姊烘潪鎵妽闁诡喖鍊垮顐㈩吋閸涱亝鏂€闂佹悶鍎弲婵嬵敊閺囥垺鐓涘璺猴功婢ф洖顭胯閺咁偆鍒掗弮鍫晢濞达綀娅i鏇㈡⒑閸涘﹦鐭婇柛鐔跺嵆楠炲啯绺介崨濠勫幐婵炴挻鑹惧ú銈夊几濞戙垺鐓冮柦妯侯樈濡偓婵犳鍠掗崑鎾绘⒑閹稿海鈽夐悗姘煎墴閻涱喖螖閸涱喒鎷绘繛杈剧悼椤牓寮抽柆宥嗙厵缁炬澘宕禍浼存煛娴g鏆e┑陇鍩栧鍕偓锝庝簴閸嬫捇宕奸弴鐔哄幗濠碘槅鍨甸崑鎰暜濞戙垺鐓熼柟鎹愭硾閺嬫盯鏌$仦璇插闁宠鍨垮畷鍗炍熺紒妯衡偓鐑芥⒒娴e憡鍟為拑閬嶆煙閸涘﹤鈻曠€殿喖顭烽幃銏㈠枈鏉堛劍娅撻梻浣藉吹閸犳劕顭垮鈧崺娑欏緞閹邦厸鎷洪柣鐘叉礌閳ь剙纾禒顓㈡⒑閸濆嫯顫﹂柛鏂跨箻閹﹢骞掗弮鍌滐紳闂佺鏈悷褔宕濆澶嬪珔閺夊牄鍔庣弧鈧梺闈涚箚閳ь剙纾导灞解攽椤旂》宸ユい顓炲槻閻g兘骞掗幋鏃€鐎婚梺瑙勬儗閸樺€熲叺濠电姷鏁告慨浼村垂婵犳艾绠犻柟鍓х帛閺呮繃銇勮箛鎾愁伀闁哄棴绠撻弻鐔告綇閸撗呮殸閻庣懓鎲$换鍐Φ閸曨垰鍐€闁靛鍔岄ˉ婵嬫⒑鐠囪尙绠伴柨鏇ㄤ簻铻為柛娑欐儗閺佸啴鏌曡箛濞惧亾閹颁焦袩闂傚倷鑳堕幊鎾绘儍閻戣棄鐤鹃柣妯款嚙缁犳牗淇婇妶鍛櫣闂佸崬娲弻锟犲炊閳轰焦鐏侀梺鍛婎焽閺佽顫忔繝姘<婵﹩鍏橀崑鎾诲箹娓氬洦鏅銈嗘尪閸ㄥ湱绮堟径灞稿亾楠炲灝鍔氭い锔垮嵆閹繝宕橀瑙f嫼闂佸壊鐓堥崳顕€宕曡箛鏇犵<婵°倓绀佸ù顔戒繆椤愶紕鍔嶇€垫澘瀚伴獮鍥敇閻樻彃姹插┑鐘垫暩婵炩偓婵炰匠鍏炬稑鈻庨幘鎶芥7濠电偛妯婃禍婵嬫偂閺囥垺鐓熼柡鍌涘閹牆霉閻樿鎲鹃柡灞糕偓宕囨殕闁逞屽墴瀹曚即寮介婧惧亾娴g硶妲堟慨妤€妫欓崓鐢告⒑閸涘娈橀柛搴㈠姍瀵爼骞栨担鍏夋嫽婵炴挻鍩冮崑鎾寸箾娴e啿鍘惧ú顏勎ч柛銉到娴滅偓鎱ㄥ鍡椾簻鐎规挸妫濋弻锝呪槈閸楃偞鐏撻梺閫炲苯澧剧紓宥呮缁傚秹寮介鐐靛摋婵炲濮撮鍡涙偂閺囥垺鐓冮柍杞扮瑜颁線鏌熸潏鎯х槣闁轰礁锕弻鐔兼倻濮楀棙鐣烽梺缁樻尵閸犳牠鐛弽顬ュ酣顢楅埀顒勫焵椤戞儳鈧洟鈥﹂崶顒€绠涙い鎾跺Х椤旀洟姊洪崨濠勬噧妞ぱ€鍋撻梺鍏煎濞夋洟鍩€椤掑喚娼愭繛鍙夘焽閹广垽宕掗悙鑼幒闁瑰吋鐣崐妤呮偪閳ь剟姊洪幐搴g畵闁瑰啿绻橀、姗€宕归瑙勬杸闂佺粯鍔曞Ο濠囧吹閻斿皝鏀芥い鏃囧Г鐏忥附銇勯姀锛勫⒌妤犵偛娲鍫曞箰鎼达絺鍋撻鍕拺闁硅偐鍋涢崝鎾煕閹炬潙鍝洪柟顕嗙節閹垽宕楅懖鈺佸箥闂傚倷绶¢崣蹇曠不閹寸偞娅犲ù鐓庣摠閻撳啴鎮归崶顏勭毢闁诲繗浜槐鎺撴綇閵娿儲璇為梺璇″枓閺呯娀骞栬ぐ鎺濇晝闁靛浚婢佺槐锕傛⒑鐠囨彃顒㈡い鏃€鐗犲畷鏉库槈閵忊晜鏅悷婊勬瀹曟椽濡烽敃鈧欢鐐烘煙闁箑澧绘繛鐓庯躬濮婅櫣绱掑Ο鏇熷灱閵囨劙宕橀鍡欑劸濡炪倖娲嶉崑鎾存叏婵犲嫮甯涚紒妤冨枛閸┾偓妞ゆ巻鍋撴い顓炴穿椤﹀綊鏌嶉妷顖滅暤鐎规洖銈告俊鐑藉Ψ瑜濈槐鐢告⒒娴g懓鍔ゆ繛瀛樺哺瀹曟垿宕熼锝嗘櫔闂備緡鍓欑粔鐢告偂閺囥垺鐓忓鑸得弸娑橆熆瑜滈崹鍫曞蓟瀹ュ鐓ラ悗锝庝簽娴煎矂鎮楀▓鍨灈闁绘牕銈搁獮鍐ㄢ枎閹惧磭楠囬梺瑙勬儗閸樹粙藟鐎n偂绻嗛柣鎰典簻閳ь儸鍛闁挎繂顦伴埛鏃堟煕閺囥劌骞楃€规洖寮剁换娑㈠箣閻戝洣绶甸梺鍝ュ枎閹冲繘濡甸崟顖氱睄闁稿本鑹炬禒妯肩磽娓氬洤浜滅紒澶婄秺楠炲啫螖閳ь剟鍩㈤幘璇插瀭妞ゆ梻鏅禍顏呬繆閻愵亜鈧倝宕㈡ィ鍐ㄧ婵☆垯璀﹂崵鏇熴亜閹板墎鐣辩紒鐘崇⊕閵囧嫰骞樼捄杞版埛缂備焦鍔楅崑鐐垫崲濠靛鍋ㄩ梻鍫熷垁閵忋倖鍊垫慨妯煎帶濞呭秶鈧鍠栭悥濂哥嵁閺嶃劍濯撮柛蹇擃槹鐎氳棄鈹戦悙鑸靛涧缂傚秮鍋撳┑鐐叉嫅缁插潡寮灏栨婵炲棗绉崇花濠氭⒑闂堟侗鐒鹃柛搴㈢叀瀹曠敻宕堕浣哄幍濡炪倖鏌i崝宀€鈧凹鍠氬褔鍩€椤掑嫭鈷戦柟鑲╁仜閸旀﹢鏌涢弬鍧楀弰鐎规洩缍佸畷鍗炍旀繝鍐ㄧ槣闂備線娼ч悧鍡椢涘▎鎴滅剨妞ゅ繐鐗婇悡鏇㈡煏婵犲繘妾柕鍥ㄧ箞閺屾盯鍩¢崒婊勫垱濡ょ姷鍋涢澶愬极閸岀偞鍋╅悘鐐舵缁犮儲绻濈喊妯活潑闁稿锕妴鍌炴晝閸屾稑鈧潡鏌ㄩ弴鐐扮椽闁搞儺鍓氶崐濠氭煠閹帒鍔楅柟宄版惈椤啴濡堕崱妯虹樂闂佸憡鍔︽禍娆撴偨閼姐倗纾介柛灞剧懆閸忓瞼绱掗鍛仯缂侇喗鐟╅獮鎺懳旈埀顒傜不椤栫偞鐓曟繛鎴炵懄缂嶆垹绱掗埀顒勫礃椤旂晫鍘卞┑鐐叉濞存艾危閻戞ǜ浜滈柨鏇炲€烽幉鐐叏婵犲啯銇濋柡灞芥嚇閹瑩鎳犵捄渚純濠电姭鎷冪仦鐣屼画婵烇絽娲ら敃顏堛€侀弴銏狀潊闁绘娅曢鍕⒒娴i涓茬紒韫矙瀹曟煡寮婚妷顖滅◤濠电姴锕ら悧鍡涙倿閸偁浜滈柟鐑樺灥椤忋儵鏌嶈閸忔稓绮堟笟鈧崺銏℃償閵娿儳顔掗梺鍛婂姌鐏忔瑩宕惔鈾€鏀介柣姗嗗枛閻忚鲸銇勯弴鐔哄⒌鐎规洖缍婂璺何涢崹顐c仢闁轰礁鍟村畷鎺戔槈濡湱鏆楅梻鍌欑閹碱偄煤閵忋倕鍨傛繛宸簼閸嬪倹绻涢崱妯诲鞍闁绘挻鐟ラ湁闁挎繂鎳庨弳鐐烘煟濠垫劒绨肩紒缁樼洴瀹曘劑顢橀悢閿嬵仩闂備礁鐤囬~澶愬垂閸ф鍨傞柟顖嗗懏娈鹃梺鎼炲劵缁犳帒顬婇幖浣光拻闁稿本纰嶉幖鎰亜閿旂偓鏆€殿喖顭烽弫鎰板川閸屾粌鏋涚€规洖缍婇、娆撳礂閻撳骸濮冮梻鍌氬€峰鎺旀椤旀儳绶ら柛褎顨呯壕鍧楁煏閸繍妲哥紒鐘靛仱閺屾洘绻濊箛鎿冩喘缂備讲妾ч崑鎾绘⒒娴e憡鍟為柛鏂跨箻瀵剟宕掑☉姘兼祫闂侀潧绻掓慨鍫ュ籍閸喎浜归梻鍌氱墛缁嬫劕鈻介鍫熲拺闁告稑锕ラ埛鎰版煟濡ゅ啫鈻堥柣娑卞櫍瀹曞崬鈽夊Ο鑲╂綁闂備礁澹婇崑鍛崲瀹ュ拋鐒藉┑鐘插亞濞撳鏌曢崼婵嬵€楀ù婊€绮欓弻娑㈡偐閸愭彃鎽甸悗瑙勬礃濠㈡﹢锝炲鍫濈劦妞ゆ巻鍋撴い顐㈢箲缁绘繂顫濋鍌︾床婵犵數鍋涘Λ娆撳垂閸偂绻嗗ù鐘差儐閳锋垿鎮归崶锝傚亾閾忣偆浜梻浣虹帛閻楁粓宕㈣閹儳鐣¢幍铏杸闂佺硶鍓濋悷锕€鈻撻弴銏♀拺闂侇偆鍋涢懟顖涙櫠閻楀牅绻嗛柛娆忣槸婵秹鏌熼鐣屾噮闁逞屽墴濞佳囧箺濠婂牊鍎婇柛顐犲劜閳锋垿鏌熼懖鈺佷粶闁告柡鍋撻梻浣告啞娓氭宕归崡鐐愭帡宕堕浣叉嫽闂佺鏈悷锔剧矈閻楀牄浜滈柡鍥╁枔婢х數鈧娲濋~澶愬箚閺冨牆惟闁靛鍎抽悰鈺備繆閻愵亜鈧牕顫忔繝姘柧妞ゆ劧绠戠痪褎绻涘顔荤凹闁抽攱甯¢弻娑氫沪閸撗勫櫘濡炪倧璁f俊鍥╂閹炬剚鍚嬮柛婊冨暢閸氼偊鎮楀▓鍨灁闁告梹鍨甸悾鐑芥晸閻樺啿鈧鏌涢埄鍐剧劷缂佸绶氬缁樻媴閽樺鎯為梺鍝ュУ閸旀鍩€椤掍浇澹橀柣妤€妫濋崺銉﹀緞閹邦剦娼婇梺缁樕戦鏍f导瀛樷拻濞撴埃鍋撴繛浣冲棗娅i梻浣告啞濞诧箓宕滈敃鍌氱柈閹兼番鍔嶉埛鎺楁煕鐏炲墽鎳呯紒鎰⒐缁绘稒鎷呴崘鍙夘棞妞ゃ倕鍊垮缁樻媴閸涘﹥鍎撻梺鐟板暱椤﹂潧顕i弻銉﹀亹鐎瑰壊鍠栧▓銊ヮ渻閵堝棗濮х紒鑼舵硶瀵囧焵椤掑嫭鈷戦柟鑲╁仜閸旀﹢鏌涢弬娆炬█妤犵偛绻戠换婵嗩潩椤撴稒瀚肩紓鍌欑椤戝棛鈧瑳鍐胯€垮ù鐓庣摠閻撴洟鏌熺€涙绠樼紒澶庢閳ь剝顫夊ú婊堝极婵犳艾绠栭柕蹇嬪€曠粈鍌炴煠濞村娅呮鐐村姍濮婄粯鎷呴搹骞库偓濠囨煕閹惧绠為柡浣稿暣閸┾剝鎷呴崣澶屼簴婵犵數濮撮敃銈団偓姘煎弮瀹曪綀绠涢幘顖涙杸闂佺粯蓱瑜板啴顢旈锔藉仺妞ゆ牗绋撳ú鎾煛瀹€鈧崰搴ㄦ偩閿熺姵鍋嬮柛顐g箖椤忥紕绱撻崒娆戝妽妞ゃ劌鐗撳畷浼村冀椤撴壕鍋撴担绯曟婵☆垶鏀遍~宥呪攽閻愬弶顥為柛鏃€鐗犻、娆愬緞婵炵偓鏂€闂佺粯锚閻忔岸寮抽埡浣叉斀妞ゆ棁顕у畵鍡欌偓瑙勬礉椤鎹㈠┑鍡╂僵妞ゆ帒鍊婚弸鍐⒒娴g儤鍤€濠⒀呮櫕閸掓帡顢涢悙鑼紱闁诲函缍嗛崰妤呮偂濞嗘挻鐓欓悷娆忓婵洭鏌涘顒佽础闁逞屽墲椤骞愭搴㈩偨婵娉涢拑鐔兼煟閺傚灝鎮戦柛濠囨敱閵囧嫰骞掑澶嬵€栨繛瀵稿閸ャ劉鎷洪柡澶屽仦婢瑰棝藝閿曞倹鐓曞┑鐘插€归崑銉р偓娈垮枦椤曆囧煡婢舵劕顫呴柣姗€娼ф慨鍫曟⒒娴e憡鍟為柛鏃€顨婂畷鎴﹀箻缂佹ê浠奸梺鍏肩ゴ閺呮繄澹曢挊澹濆綊鏁愰崨顔跨闂佸疇妫勯ˇ杈╂閹烘梻纾兼俊顖氭禋娴滎亪鏁愰悙鍓佺杸婵炴垶鐟﹂崕顏堟⒑闂堚晛鐦滈柛姗€绠栭幃锛勨偓锝庡枟閳锋垹绱掗娑欑濠⒀冨级閵囧嫰濡搁妷锕€娈楀銈冨灪濮婂鍩€椤掍胶鈯曟い顓炴川缁粯銈i崘鈺冨幈濡炪倖鍔戦崐鏇㈠几閹寸姷纾奸柍褜鍓涢埀顒婄秵閸犳鎮″☉銏″€堕柣鎰絻閳锋棃鏌曢崱妯烘诞闁哄苯绉烽¨渚€鏌涢幘鍗炲缂佽京鍋ゅ畷鍗炩槈濡》绱梻浣告惈缁嬩線宕㈤懖鈺冧笉闁挎繂顦伴悡銉╂煛閸ヮ煈娈斿ù婊呭亾娣囧﹤螖閳ь剟骞婂Ο渚綎婵炲樊浜滃婵嗏攽閻樻彃鏆欐い锔规櫊濮婃椽骞栭悙鎻掝瀱闂佸憡顨呴崯鍧楁偩閻戣姤鏅搁柣妯挎珪閸庮亜顪冮妶鍡楀Ё缂佽鲸娲滅划璇差潩閼哥鎷洪梻鍌氱墛缁嬫挻鏅堕弴銏$厱濠电姴鍊归崯鐐电磼閸屾氨效闁诡喗鐟╅、妤呭磼濠婂骸鏅梻浣筋嚙鐎涒晝绮欓幒妞烩偓锕傚炊椤掍礁鍓归柣搴秵閸犳鎮¢弴銏犵婵烇綆鍓欓悘鈺呮煃缂佹ɑ绀嬮柡灞剧洴閸╋繝宕橀妸銈嗩潟婵°倗濮烽崑娑㈩敄婢舵劕鏋侀柛灞剧矌绾惧吋淇婇婊呭笡闁绘繐濡囩槐鎾诲磼濞嗘帒鍘¢梺鎯х箰闁帮絽鐣烽姀掳鍋呴柛鎰╁妿椤ρ冣攽閳藉棗鐏犻柛姘儔椤㈡洘绂掔€n偆鍘告繝銏f硾椤戝懘鎮樺澶嬬厸闁逞屽墯缁傛帞鈧綆鍋嗛崢浠嬫⒑瑜版帒浜伴柛鎾寸懅閻ヮ亣顦归柟顔筋殔椤繈顢楁担鍛婎仱缂傚倷娴囨ご鎼佸箰閹间緡鏁囧┑鍌滎焾缁€瀣亜閹捐泛啸鐎规洘鐓″缁樻媴閾忕懓绗℃繛鎾寸椤ㄥ﹤鐣烽弶搴撴婵ê褰夌粭澶娾攽閻愭潙鐏﹂懣銈嗕繆閹绘帞澧涚紒缁樼洴瀹曞崬螖閸愵亶鍚呮繝娈垮枦椤銆冩繝鍌ゆ綎婵炲樊浜濋崵鎺楁煏閸繃鍟楅柕蹇ョ磿缁犵偓绻涢弶鎴剱婵炲懎娲ら湁婵犲﹤鎷嬮悞楣冩煃鐠囨煡鍙勬鐐寸懇瀹曟﹢鍩¢崒娑氬綗闂備浇顕ф鎼佸储濠婂牆纾婚柟鍓х帛閻撴洟鏌¢崶銉ュ闁告ɑ鎸抽弻鐔兼煥鐎n偁浠㈠┑顔硷攻濡炶棄螞閸愵喖鐓涘ù锝囧劋琚欓梻鍌欑閹诧繝鏁嬮梺闈涚墢椤牓鎮惧畡鎵虫斀闁割偅鑹炬禍楣冩煥濠靛棝顎楅柡瀣枛閺岋綁骞樼€涙顦伴梺鍝勬湰濞叉鎹㈠☉銏犲瀭妞ゆ梻鍘ц闂傚倷鑳剁涵鍫曞疾椤忓棛绀婂〒姘e亾鐎殿喖顭烽幃銏㈠枈鏉堛劍娅栨繝鐢靛仜濡瑩宕硅ぐ鎺撳仒闁靛繈鍊栭埛鎴﹀级閻愭潙顥嬮柛鏂跨Ч閺屾盯寮埀顒勬偡閵夆晜鍋╅柣鎴f闁卞洭鏌¢崶鈺佷户闁告ɑ鎮傚娲川婵犲倸顫戝┑鐐差槹濞茬喎顫忔繝姘兼晬闁绘劗琛ラ幏濠氭⒑缁嬫寧婀伴柣鐔村姂瀹曟浠︽穱鍙樼盎濡炪倖鎸鹃崑鐔告櫠閿旈敮鍋撳▓鍨灓闁轰礁顭烽妴浣肝旈崨顓狀槹濡炪倖宸婚崑鎾寸箾閸垹浠﹀ǎ鍥э躬婵℃儼绠涢弴鐐茬厒闂備礁鎽滈崳銉╁磻婵犲洤绠栭柣鎰惈閸ㄥ倹銇勯幇顔夹$紒銊ヮ煼濮婃椽鎮烽悧鍫熷創濠碘槅鍋呴〃鍡欑矉瀹ュ棎鍋呴柛鎰ㄦ杹閹疯櫣绱掔紒銏犲箹闁瑰啿姘﹂。璺ㄧ磽閸屾瑧璐伴柛鐘崇墵閺屽﹪鏁愰崨顖涙濠殿喗顭堝▔娑氱不閾忣偂绻嗛柕鍫濆€告禍鍓х磽娓氬洤浜滅紒澶婄秺瀵鈽夐姀鈺傛櫇闂佹寧绻傚ú銊╂偩閸忛棿绻嗛柕鍫濇搐瀛濆┑鐐叉▕閸樺ジ锝炶箛鎾佹椽顢旈崨顓濈敾闂備浇顫夐鏍窗濡ゅ懏鍊垫い鏂跨毞閺€浠嬫煟閹邦剙绾ч柛锝囧劋缁绘盯宕f径宀€鐓傞梺鍛婂笚鐢帡鍩㈡惔銊ョ鐎规洖娴傞崥鍛存⒒娴g懓顕滄繛鎻掔Ч瀹曟垿骞樼紒妯煎幗闂佽宕橀幓顏堟嚀閸ф鐓涚€光偓閳ь剟宕伴幇顒夌劷闊洦绋戠粈鍫㈡喐韫囨稑姹查柣妯哄棘閺冨牊鍋愰梻鍫熺◥閺夘參姊洪幖鐐插婵炲拑缍侀獮鎴﹀閻橆偅顫嶉梺闈涚箳婵挳鎳撻崹顔规斀闁宠棄妫楅悘鐘绘煙绾板崬浜伴柨婵堝仜椤撳ジ宕担鐟扮槣闂備線娼ч悧鍡椢涘▎鎾崇厱闁归偊鍘剧粻楣冩煕濞嗗浚妯堥柣鎺嶇矙閺岀喖鐛崹顔句患闂佸疇顫夐崹褰掑焵椤掑﹦绉甸柛瀣缁傛帒煤椤忓應鎷婚梺绋挎湰濮樸劍鏅跺☉銏$厱闁瑰搫妫楁禍楣冩⒒娓氣偓濞佳呮崲閸儱纾归柡宥庡幗閸嬪倿鏌曟径鍡樻珕闁绘挻鐩弻娑㈠Ψ椤旀儳甯掑銈呯箰閻楀棝鎮為崹顐犱簻闁瑰搫绉烽崗宀€绱掗悩铏磳闁哄矉缍侀弫鎰板炊瑜嶉獮瀣渻閵堝啫鐏柣鈺婂灦楠炲啫鈻庨幘宕囬獓闂佺懓鐡ㄧ划宥夋儓韫囨稒鈷掑ù锝堟閸氱懓鈹戦鑺ョ稇閻撱倝鏌ㄩ弴姘舵濞存粌缍婇弻娑㈠箛闂堟稒鐏堥梺鍛婅壘缂嶅﹪寮婚悢鍛婄秶濡わ絽鍟宥夋⒑缂佹ɑ灏伴柣鐔叉櫊瀵鈽夊鍛澑濠殿喗锕╅崗娑樞уΔ鍛拺闁告繂瀚ˉ鐐烘煥閺囨ê鐏茬€殿喛顕ч埥澶愬閻樻剚妫熼梺鑽ゅУ娴滀粙宕滄潏顐▌闂佸搫鐬奸崰鏍€佸▎鎾崇濠㈣泛锕f竟鏇㈡⒑閸濆嫬鈧爼宕曢弻銉﹀€靛┑鐘崇閳锋垿鎮峰▎蹇擃仼闁告柣鍊栭妵鍕即閵娿儱绫嶉悗瑙勬磸閸ㄤ粙骞冩禒瀣窛濠电姴瀚獮妤呮⒒娴h櫣甯涢柡灞诲姂楠炴顭ㄩ崼婵堢枃闂佸憡鍔﹂崰妤呭磹閸偅鍙忔俊顖滃帶鐢泛顭胯閸ㄥ爼寮婚悢鍝ョ懝闁割煈鍠栭~鍥倵鐟欏嫭绀€闁靛牆鎲¢幈銊╁焵椤掑嫭鐓忛煫鍥э攻椤绱掗幍浣稿⒉濞e洤锕幃娆擃敂閸曘劌浜鹃柡宥庡幖缁犳澘螖閿濆懎鏆欑痪鍓х帛缁绘盯骞嬪▎蹇曚患闂佺粯鎸诲ú鐔煎蓟閿熺姴绀冮柕濞垮劗閸嬫捇鎳¢妶鍜佹婵犻潧鍊婚…鍫㈢棯瑜旈弻娑㈩敃閿濆洠妲堟繝寰枫倕浜圭紒杈ㄥ笒铻栧ù锝呮贡濞堛倗绱撴担浠嬪摵閻㈩垱甯熼悘鍐⒑閸涘﹤濮傞柛鏂跨Ч閹宕滆绾捐棄霉閿濆牊顏犻悽顖涚〒缁辨帞鎷犻懠顒€顣洪梺浼欑悼閸忔﹢骞冮姀銏犳瀳閺夊牄鍔嶅▍宥夋⒒娴h櫣甯涢柡灞诲妽缁旂喐绻濋崶褏鏌堥柣蹇曞仜婢х晫寮ч埀顒勬⒑濮瑰洤鐏叉繛浣冲嫮澧″┑锛勫亼閸婃牕顫忚ぐ鎺撳亱闁绘灏欓弳锕€霉閸忓吋缍戦柛鎰ㄥ亾婵$偑鍊栭幐楣冨窗閹邦兘鏋嶉柛銉墯閳锋垿姊婚崼鐔剁繁闁绘帡绠栭弻娑欐償椤斿吋鐝濋悗娈垮枤椤牓顢橀崗鐓庣窞閻庯綆鍓欏铏節閻㈤潧鈻堟繛浣冲吘娑㈩敇閻愬稄缍佸畷顐﹀Ψ瑜忛敍婊堟⒑缂佹﹫鑰挎繛浣冲洤鍑犳繛鎴欏灪閻撴稓鈧厜鍋撻柍褜鍓熷畷浼村箻閼告娼熼梺鍦劋椤ㄥ懘锝為崨瀛樼厽婵☆垵娅i敍宥吤瑰搴濈敖缂佽鲸鎹囧畷鎺戔枎閹烘繂鏁奸梻浣侯焾椤戝棝骞戦崶顒€绠栨俊銈呮噺閺呮煡骞栫划鍏夊亾閼碱剚瀵滄繝鐢靛仜閻°劎鍒掑鍥у灊闁规崘顕ч拑鐔兼煟閺冨偆鐒炬い鏇憾閹鈽夊▍铏灴閺屻劑顢橀悢铏诡啎闁诲孩绋掗…鍥儗鐎n剛纾奸悹鍥ㄥ絻閺嗭絽鈹戦敍鍕毈鐎规洜鍠栭、娑樞掔粭鍝勫闁哄本娲樺鍕熼悜妯间邯闂備礁鎲¢幐鐑藉础閸愬樊娼栭柧蹇撳帨閸嬫捇宕烽鐑嗏偓灞剧箾閸忕厧濮嶉柡灞剧洴婵℃悂濡烽敃鈧禒鏉懳旈悩闈涗粶闁哥喐鎸冲畷娲晸閻樺弶銇濇繛杈剧秬椤鈻嶉崶顒佲拻濞达絿鎳撻婊呯磼鐠囨彃鈧潡鐛箛鏇楀亾閿濆骸鏋涢柣鎺戠仛閵囧嫰骞掗崱妞惧缂傚倷鑳剁划顖炴晪濡炪値鍋勭换鎰弲濡炪倕绻愮€氼剛绮e☉娆戠瘈闁汇垽娼у瓭闂佸摜鍠嶉崡瀹犳闂侀潧顦弲婊堝煕閹达附鍋i柛銉簻閻ㄨ櫣绱掗悩鍝勭毢闁逞屽墮閸樻粓宕戦幘缁樼厵闂傚倸顕ˇ锔剧磼閻樺磭澧甸柡宀€鍠撶划娆撳箰鎼淬垹闂梻浣藉吹閸犲海绱炴繝鍥ц摕鐎广儱鐗滃銊╂⒑閸涘﹥灏伴柣鐔叉櫊閺佹劙鎮欓崜浣烘澑濠电偞鍨堕悷锕傚磿椤忓牊鈷戦柤濮愬€曢弸鎴炵節閵忊槄鑰挎い銏′亢椤﹁鎱ㄦ繝鍐┿仢鐎规洦鍋婂畷鐔碱敆閳ь剛绮e☉銏♀拺闁告縿鍎辨牎闂佸憡姊归悷鈺呯嵁閸愵喗鍋ㄧ紒瀣仢瀹撳棝姊洪棃娑氱畾婵$嫏鍥х婵炲樊浜濋埛鎴犵磽娴e顏堟倶瀹ュ鐓涢柛娑卞枤閻﹪鏌嶇拠鑼ф鐐搭焽缁辨帒螣閻撳骸绠為梻鍌欑窔濞佳団€﹂崼銉ョ?闁规儼妫勯弰銉╂煥濠靛棭妲归柣鎾寸懄閵囧嫰寮崶璺烘閻庤鎸稿Λ娆撳Φ閸曨垰顫呴柍銉ュ暱閹界敻姊虹化鏇熸澒闁稿鎸搁—鍐Χ閸℃鐟ㄩ柣搴㈠嚬閸犳牠鎮鹃崹顐ょ懝闁逞屽墴瀵鎮㈤崗鐓庘偓缁樹繆椤栨粌鍔嬫い鏃€娲熷娲传閸曨偅娈梺缁橆殔濡繈骞冮悙鍝勫瀭妞ゆ劗濮崇花濠氭⒑閸︻厼鍔嬮柛銊ф暬閸┾偓妞ゆ帒鍊荤敮娑氱磼鐎n亶妲告い鎾冲悑瀵板嫮鈧綆鍓欓獮妤佺節绾版ɑ顫婇柛銊ф暬瀹曟垿骞囬鑺ユ濠电偞鍨崹娲偂閻斿吋鐓欓柟顖嗗拑绱炵紓浣哄С閸楁娊寮诲鍥ㄥ枂闁告洦鍋嗘导宀勬⒑鐠団€虫灍闁荤啿鏅犻獮濠囨偐濞茬粯鏅為梺鍏煎墯閸ㄩ亶顢撳Δ鍛拻闁稿本鐟чˇ锕傛煙鐠囇呯瘈鐎殿喖顭烽弫鎰緞婵犲嫸绱繝寰锋澘鈧洟宕鐑囩稏闁哄洢鍨洪悡娆撴煟閹寸倖鎴犱焊椤撶姷纾奸柛鎾茬娴犻亶鏌熼绛嬫疁闁轰焦鍔栭幆鏃堝灳閼碱剚瀵滄繝鐢靛仜椤曨厽鎱ㄦ导鏉戝瀭闁芥ê顦藉鏍ㄧ箾瀹割喕绨诲ù鑲╁█閺屾盯寮撮妸銉よ埅濠德ゅ皺閺佽顫忓ú顏勫窛濠电姴鍟棄宥囩磽娴g瓔鍤欓柣妤佹崌閹即顢欑捄銊ф澑濠电偞鍨堕敋缂佹劖鐩弻锝嗘償閵忊懇濮囬梺鎸庤壘闇夐柣娆屽亾闁告瑥鍟~蹇撁洪鍕炊闂佸憡娲栭悘姘櫏濠碉紕鍋戦崐鏍垂閸洘鍋¢柕澶嗘杹閳ь剨绠撳畷鎯邦檨婵炲皷鏅犻弻銈夊传閵夛附姣勯梺鍛娒肩划娆撳蓟閻旂厧绀傞柤娴嬫櫆濞堫剟姊虹粙娆剧劸闁稿﹥娲熼垾锕傚炊椤掆偓缁犳稒銇勯幘璺盒ユい鏃€娲熷娲川婵犲嫭鍣у銈忕畳妞存悂寮查崼鏇燁棃婵炴垶甯楅弬鈧梻浣哄仺閸庤京澹曢銏犳槬闁挎繂妫▓浠嬫煟閹邦剦鍤熷褜鍓熼弻鐔风暋閻楀牆娅ч梺鍝ュТ閿曘倛鐏掗柡澶屽仦濠㈡﹢藟濮橆兘鏀介柣鎰摠鐏忎即鏌涢埡浣告殻鐎规洘鍨块獮姗€宕瑰☉妯瑰濠电偛鐗嗛悘婵嬪几閻斿吋鐓欐慨婵嗘湰閻濐亪鏌熸笟鍨闁糕斁鍋撳銈嗗笒鐎氼參鎮¢崘顔界厓閺夌偞澹嗛ˇ锕傛煛閸℃瑥浠遍柡宀嬬到閳规垿宕惰閺嬫瑥鈹戦纭峰姛缂侇噮鍨堕獮蹇涘川椤栨稑鏋傞梺鍛婃处閸嬪倿宕Δ鍛拻濞达絼璀﹂悞楣冩倵閸偄娴€规洘濞婇弫鎰板椽娴e憡顓挎俊鐐€栭崝褏绮婚幋锔藉亗婵炴垯鍨洪悡鏇熺箾閹存繂鑸归悽顖ょ秮閺屾洘绻涢悙顒佺彆闂佺粯鎸搁崯鎾蓟濞戞ǚ鏀介柛鈩冾殢娴犲ジ姊洪柅鐐茶嫰婢т即鏌℃担鍓茬吋闁绘侗鍠涚粻娑㈠籍閸屾粎妲囨繝娈垮枟閿曗晠宕㈤幖浣哥闁惧繐婀辩壕钘壝归敐鍛棌闁稿孩鍔欓幃妤冪箔濞戞ê鏋﹂柤鏉跨仢闇夐柣鎾虫捣閹界娀鏌i幘璺烘灈闁哄矉缍佸顕€鍩€椤掆偓椤洤鈻庨幇顓炲伎闂佺鏈竟鏇㈠磻閹捐埖鍠嗛柛鏇ㄥ墰椤︺劌顪冮妶鍐ㄥ闁绘锕︾划瀣箳濡や焦娅嗛梺浼欑到婢跺洭寮ㄩ幎鑺モ拺闁告稑锕﹂幊鍕亜椤撶偞鍠橀柟顖氬閹棃锝為鐘电暰闂備胶绮崝锔界濠婂牆鐒垫い鎺嶈兌婢у灚顨ラ悙鏉戝闁靛牞缍佸畷姗€濡歌缁遍亶姊绘担铏瑰笡闁哄被鍔戦獮澶愬灳閺傘儲鐎洪梺缁橆焽缁垶鎮¢妷鈺傜厸闁稿本渚楅崕銉︾箾閼测晛鏋庨棁澶嬬節婵犲倸顏柣顓熷浮閺岋紕浠﹂悙顒傤槷缂備胶濮甸惄顖涗繆閻ゎ垼妲鹃梺鎸庣〒閸犳劗鎹㈠┑瀣厱闁逞屽墴瀹曘劑顢欓懞銉ф闂傚倷绶氶埀顒傚仜閼活垱鏅堕崣澶堜簻妞ゆ劑鍩勫Σ鎼佹偂閵堝鐓涚€广儱楠搁獮妤呮煕鐎n亶妯€闁哄本绋栫粻娑樷槈濞嗘瑧鍚圭紓鍌欐祰椤曆兾涘▎鎾崇疄闁靛鍎弨浠嬫煕閳╁啰鎳呴柛鏃傤焾閳规垿鍨鹃崘鑼獓闂佺瀛╂繛濠囧灳閺冨牆绀冩い鏂挎瑜旈弻娑㈠焺閸忥附宀搁獮蹇涙偡閹佃櫕鏂€闂佺粯鍔樺▔娑㈡儍濞差亝鐓曢柣妯荤叀閸欏嫰鏌ㄥ┑鍫濅哗缂佺姵鐩獮妯绘媴鐟欏嫨浠㈠銈冨灪濡啫鐣烽妸鈺婃晬婵﹩鍎烽妷鈺傗拻闁稿本鐟ㄩ崗宀€绱掗鍛仸鐎规洘绻傝灒闂傚倸顕崜銊ヮ渻閵堝懐绠版俊顐㈢焸瀹曟垿骞橀幇浣瑰兊濡炪倖鎸鹃崰鎾诲礄閳ユ剚娓婚柕鍫濋瀵劑鏌涙惔鈽嗙吋閽樻繈鏌熼幆鏉啃撻柣鎾寸懇閺屾稑鈽夊鍫濅紣闂佸磭绮ú婊堝焵椤掍緡鍟忛柛鐘崇墵閳ワ箓鎮滈挊澶婄€梺璇″瀻閸涱喗顔曢梻浣规偠閸庮垶宕濆澶嬪仼闁绘垼濮ら埛鎴︽偣閸ャ劌绲婚柛銈堜含缁辨挸顓奸崨顕呮&閻庤娲樼划宀勫煡婢舵劕顫呴柍鈺佸暞閻濐偊姊绘担铏瑰笡闁哄被鍔戦獮妤€顭ㄩ崨顖欑瑝婵°倧绲介崯顖炲磹閻㈠憡鐓熼柕蹇婃閸熷繘鏌i幒鏂夸壕闁靛洤瀚幆鏃堝閳ヨ櫕娈紓鍌欐祰妞村摜鏁敓鐘茬畺闁冲搫鎳忛幆鐐淬亜閹扳晛鐏い锝嗙叀濮婄粯鎷呮搴濊缂備浇寮撶划娆忕暦閺屻儱钃熼柕澶嗘噰閸嬫捇鏁冮崒姣尖晠鏌嶆潪鎵槮闁兼澘娼″娲礃閸欏鍎撻梺绋匡攻閸旀瑦淇婇悜钘壩ㄩ柕蹇婂墲閺夋悂姊绘担铏瑰笡閽冮亶鏌涢幘鏉戝摵鐎规洦鍨电粻娑樷槈濞嗘垵骞堥梻浣虹帛閿氱痪缁㈠幗閺呭爼顢旈崼鐔蜂簵闂侀潧鐗嗗Λ搴㈢濠婂牊鐓欓柟瑙勫姈绾箖鏌涢幘褰掑摵缂佺粯鐩畷妤呮嚃閳轰讲鎷伴梻浣告惈閻瑩宕卞▎鎴炴緫婵犳鍠楅敋闁告艾顑囩槐鐐哄醇閵夛妇鍘介柟鍏肩暘閸ㄥ銆傞懠顑藉亾閸忓浜鹃梺褰掓?缁€渚€鎷戦悢琛″亾楠炲灝鍔氭い锔诲灠閺侇噣姊绘笟鈧褔鏁嶈箛鎿冨悑闁搞儮鏅╁Σ绋库攽閻樺灚鏆╅柛瀣洴椤㈡岸顢橀悢宄扮亖濡炪倖鎸堕崹褰掑磼閵娿儮鏀介柛灞剧矤閻掗箖鏌i幘杈捐€块柡宀€鍠愬蹇涘礈瑜忛弳鐘绘⒑缂佹ɑ鎯堢紒缁樼箞瀵鈽夐姀鐘靛姶闂佸憡鍔х紓姘柦椤忓棛纾藉ù锝夋涧婵″吋銇勯鐐叉Щ妞ゎ偄绻愮叅妞ゅ繐瀚槐鍫曟⒑闂堟侗妲堕柛搴㈢叀閹銈i崘鈹炬嫼闁荤喐鐟ョ€氼噣骞楅崘鈺冪闁告侗鍠楃粈鍐磼瀹€鍐摵缂佺粯绻堝畷鐔煎Ω閵夈倕顥氭繝鐢靛仦閸ㄥ爼顢旀导鏉戠闁绘劖褰冮悘渚€鏌f惔銊︽锭闁硅姤绮庢竟鏇㈠礂缁楄桨绨婚梺鍝勭Р閸斿酣鍩婇弴鐘电<闁逞屽墴瀹曟﹢顢欓悾灞藉箺闂佺鍋愮悰銉ノi崨瀛樺亗闁稿繐鍚嬮崣蹇撯攽閻樻彃鏆為柕鍥ㄧ箘閳ь剝顫夊ú婊堝礂濮椻偓閵嗕礁顫滈埀顒勫箖濞嗘挸绾ф繛鍡欏亾椤モ剝绻濋悽闈浶ラ柡浣规倐瀹曟垵鈽夐姀鐘盒曢柣搴秵閸犳宕戦敓鐘崇厪濠㈣泛妫欏▍鍛存煟閹惧绠為柡宀€鍠栭獮鎴﹀箛闂堟稒顔勭紓鍌欒兌婵敻鎯勯鐐茶摕闁挎繂鎲橀弮鍫濈劦妞ゆ帒瀚崑瀣煕閹伴潧鏋涚紒鐙€鍨辩换娑橆啅椤旇崵鍑归梺缁樻尵閸犳牠鐛弽顐㈠灊闁荤喐婢橀埛澶愭煟閻樺啿濮€闁逞屽墯閺嬪ジ寮ㄩ懞銉d簻闁哄啫娴傞崵娆戔偓瑙勬尭濡繈寮诲☉銏犵厴闁诡垎鍌氼棜婵犵绱曢崑鎴﹀磹閺嶎厼鍨傞柣鎾冲濞戙垹绀嬫い鎺戝亞濞插憡淇婇妶蹇曞埌闁哥噥鍨堕崺娑㈠箳閹炽劌缍婇弫鎰板礋椤曞懎濡抽梻浣虹帛鐢偤宕戦幘璇参﹂柛鏇ㄥ灠缁狅絾绻濋棃娑欑ォ婵☆偓绠戣灃闁绘﹢娼ф禒锕傛煕閺冣偓椤ㄥ牆危閹版澘绠抽柟鍐茬-閸犳挻绂嶉幖浣稿唨闁靛闄勫▓鐓庘攽閻樺灚鏆╁┑顔惧厴瀵偊宕ㄦ繝鍐ㄥ伎闁诲孩绋掗敋妞ゆ洟浜堕弻銊モ攽閸♀晜笑缂備緡鍋勭粔褰掑蓟瀹ュ牜妾ㄩ梺鍛婃尵閸犳牠鎮伴璺ㄧ杸婵炴垶锚缁愭盯鏌f惔銏⑩姇闁挎艾霉閻欌偓閸欏啫顫忛搹瑙勫枂闁告洟娼ч弲閬嶆⒑闂堚晝绉甸柛銊ュ暱鍗遍柟鎵閺呮繈鏌涚仦鍓р枔闁瑰嘲顭峰铏圭矙閹稿孩鎷遍梺鑽ゅ暀閸ヤ礁娲弫鍐磼濞戞艾骞嶇紓浣哄亾濠㈡ê鐣烽浣侯洸濞寸厧鐡ㄩ悡娆愩亜閺嶃劎顣叉繝鈧幍顔瑰亾閸偅绶查悗姘煎枟缁傛帡鏁冮崒娑樹患閻庡厜鍋撻柍褜鍓熼幃鍝勎熺悰鈩冩杸闁圭儤濞婂畷鎰槾鐎垫澘锕ョ粋鎺斺偓锝庝簽閺屽牆顪冮妶鍡楀闁稿﹥顨嗙粙澶婎吋閸℃ê寮垮┑鈽嗗灠閻忔繈鎮¢幇鐗堢厽闁规儳顕ú鎾煛鐏炲墽娲存鐐叉喘閸┾剝鎷呴崜鑼偓宄扳攽閻橆偅濯伴柛鏇ㄥ墰椤︿即鎮楃憴鍕闁绘牕銈搁悰顔碱潨閳ь剟銆佸▎鎾村仼閻忕偠妫勭粻銉╂⒒閸屾瑨鍏屾い顓炵墢閹广垹螖閸涱厾锛涢梺鍦濠㈡ê效閸欏鍙忔俊鐐额嚙娴滈箖姊洪崫鍕拱闁烩晩鍨辨穱濠囧箹娴h倽鈺呮煏婢跺牆鍔滈柛搴簽缁辨捇宕掑▎鎴g獥闂佸摜濮甸〃鍛扮亱闂佸憡鍔﹂崰鏍嫅閻斿吋鐓忓┑鐐戔偓閸嬫捇鏌涚€n偅宕岄柡浣瑰姈閹棃鍨鹃幇浣归獎闂傚倷妞掔槐顔剧不閹达附鍋嬮柟鐐墯濞兼牠鏌涘┑鍡楃彅鐟滄柨鐣烽幆閭︽Ь婵炲鍘ч悧鍡涘煘閹达附鍊烽柡澶婄仢閻ㄧ喖姊洪崨濠冨闁告瑥楠搁湁闁告洦鍋€閺€浠嬫煟濡鍤嬬€规悶鍎甸弻鐔煎礃瀹割喗鈻堥悗瑙勬礃閸ㄥ潡鐛鈧顒勫Ψ閿斿彞绨撮梻鍌欑婢瑰﹪鎮¢崼銉ョ獥婵°倕鎳忛崐鍫曟煕椤愮姴鍔滈柍閿嬪灩缁辨挻鎷呯拠锛勫姺婵犫拃灞奸偗闁哄本娲熷畷濂稿閳哄啫濮兼俊鐐€栧ú鈺冪礊娓氣偓閵嗕線寮撮姀鐘栄囨煕鐏炲墽鐓瑙勬礋濮婃椽骞愭惔锝囩暤婵°倗濮甸幃鍌氼嚕閹间焦鍋勯柛蹇氬亹閸樹粙姊虹憴鍕婵炲鐩绋库槈閵忥紕鍘搁悗鍏夊亾闁逞屽墴瀹曚即寮介鐘茬ウ闂佺硶鍓濋崙鐟拔f繝姘拺闁兼祴鏅╅悞鍓х磽瀹ュ拑韬€殿喛顕ч濂稿醇椤愶綆鈧洭姊绘担鍛婂暈闁规瓕顕ч~婵嬪Ω閳轰胶顔夐梺闈涚箞閸婃洟鏌嬮崶銊х瘈闁割煈鍋勬慨鍥ㄧ箾閸稑濡界紒缁樼箞閹粙妫冨ù璁圭悼閻ヮ亪寮剁捄銊愌呪偓娈垮枟閻擄繝鐛幘璇茬婵犻潧鐗嗛弫鎼佹⒑閼姐倕鞋婵炲拑绲挎禍鎼佸Ω閳轰胶顦梺缁樻煥閸氬鎮¢悢鎼炰簻闁规壋鏅涢悘鈺傘亜韫囷絽骞楅柟渚垮妽缁绘繈宕ㄩ鍛摋缂傚倷绶¢崰妤呮偡閳哄懐宓侀柟閭﹀幗閸庣喖鏌曡箛濞惧亾閹颁椒绱楅梻鍌氬€搁崐鐑芥嚄閸洖鍌ㄧ憸宥夋晝閵忋倖鐒肩€广儱鎳愰敍娑㈡⒑鐟欏嫬鍔ゅ褍閰i幆灞惧緞閹邦厾鍘甸梺缁樺灦閿氶柣鎺斿亾缁绘稓绮崫鍕潎闂佸搫鑻粔鐑铰ㄦ笟鈧弻娑㈠箻鐎靛憡鍣伴梺鎸庣箘閸嬬姷绮诲☉銏犵濞达綀顫夐妵婵囥亜閵忊剝顥堢€规洏鍔戦、姗€鎮╅幇浣插亾瀹ュ棛绡€闁汇垽娼цⅷ闂佹悶鍔庨崢褔鍩㈤弬搴撴闁靛繆鍓濆▍鍥⒑闂堟侗妲堕柛搴櫍瀵悂寮崼鐔哄幈濡炪倖鍔х徊鍓х矆閸愵喗鐓冮梺鍨儏閻忔挳鏌$仦鍓р槈闁宠鍨垮畷鐔碱敃閵忕媭娼涢梻浣告惈缁嬪嫮鎹㈠┑鍡╂綎闁惧繐婀辩壕鍏兼叏濡も偓濡瑩鎮鹃崗鑲╃瘈婵炲牆鐏濋弸鐔兼煙閸涘﹤鈻曢柕鍡曠椤繈鎳滈崹顐g彸闂備焦鎮堕崕顖炲礉瀹€鍕仧闁哄绨遍弨浠嬫煟閹邦剛鎽犵紓宥嗗灦閵囧嫰骞嬪┑鍥舵&闂佹寧绻勯崑娑㈩敇閸忕厧绶為悗锛卞嫬顏归梻鍌氬€搁崐鎼佹偋婵犲嫮鐭欓柟鎯у娑撳秹鏌涢幇顓犮偞闁衡偓閼恒儯浜滈柡鍐e亾闁稿孩濞婂畷銏⑩偓鐢电《閸嬫挾鎲撮崟顒傤槰缂備浇顕ч悧鎾绘偘椤旂⒈娼ㄩ柍褜鍓熼妴浣糕枎閹寸偛鏋傞梺鎸庣箓濡顢旇ぐ鎺撯拻闁稿本鐟чˇ锕傛煙鐠囇呯?缂侇喗鐟╅獮瀣晜閼恒儲鐝栭梻渚€娼ч悧鍡椢涘▎鎾崇煑闊洦鎼╅悢鍡涙煠閹间焦娑у┑顔肩墦閺岋綁骞樼€涙顦伴梺璇″枟椤ㄥ﹪寮幇顓熷劅闁炽儴灏欓崙褰掓煟鎼淬値娼愭繛鍙夌墵瀵敻顢楅崟顐嬶箓鏌涢弴銊ョ仩妞ゎ偄鎳橀弻宥夋寠婢跺妫ら梺鍛婃⒐閹倸顫忓ú顏咁棃婵炴垶鐟ラˇ鈺呮⒑閸涘﹥鈷愰柣鐔叉櫊閹即顢氶埀顒勭嵁閹烘嚦鏃堝焵椤掑倻涓嶇紓浣骨滄禍婊堟煛瀹ュ啫濡块柍钘夘槹閵囧嫯绠涢幘鍓佇ㄥ┑顔硷工椤嘲鐣烽幒鎴旀瀻闁规惌鍘借ⅵ闂傚倷鑳堕、濠囶敋濠婂懏顫曢柡鍥╁Т閸ㄦ繃绻涢崱妯诲碍缂佺媴缍侀弻銊╁籍閸ヮ灝鎾寸箾閸涱厽鍠樻慨濠冩そ濡啫鈽夋潏鈺佸綃濠电姷顣介埀顒冩珪閸犳﹢鏌熼鐐毈闁硅櫕绮撳畷妤呭传閵壯呮毎濠碉紕鍋戦崐鏍偋濡ゅ啰鐭欓柟鍓ь劜閼板潡鏌﹀Ο渚&闁荤喖鍋婇悡銉╂煕閺囥劌骞橀柣鎾愁樀濮婃椽宕崟顓犱紘闂佸摜濮甸幑鍥春閳ь剚銇勯幒宥堝厡闁愁垱娲橀妵鍕敇閻愭潙绐涚紓渚囧枛椤攱淇婇悜鑺ユ櫆閻犳亽鍔庨悾鐐繆閻愵亜鈧牠鎮уΔ鍛偓鍐川椤旂虎娲告俊銈忕到閸燁垶鍩涢幋锔藉仯闁搞儯鍔岀徊缁樸亜閹哄鐏柕鍥у瀵噣鍩€椤掑嫭鍋嬮柣妯垮皺閺嗭箓鏌℃径濠勬皑婵℃彃鐗撻弻鏇$疀婵犲啯鐝曢梺鍝勬媼娴滎亪骞冨畡閭︾叆闁告洦鍓﹀Λ鍐倵鐟欏嫭绀冩俊鐐跺Г娣囧﹪鎮滈懞銉︽珖闂侀€炲苯澧版繛鍡愬灲閹瑩鎮滃Ο鐓庡箥闂傚倷绶¢崣蹇曠不閹寸偞娅犵紓浣诡焽缁犻箖鏌i幘鍐插毐闂婎剦鍓氶幈銊︾節閸涱噮浠╃紓浣介哺鐢帡锝炲鍫濋唶闁挎繂鍊告禍楣冩煙缁嬫寧鎹g紒鐘冲劤闇夐柨婵嗘噹閺嗛亶鎮楀鐓庡籍鐎规洩缍€缁犳稑鈽夊▎鎴濆箞婵$偑鍊栭崝褏寰婇崜褏鐭嗛柛鎰靛枟閻撳啴姊洪崹顕呭剰缂佹甯″Λ浣瑰緞閹邦厾鍙嗗┑鐘绘涧濡瑩宕冲ú顏呯厱闁绘柨鎼禒閬嶆煛鐏炲墽娲撮柟顔哄灲瀹曨偊宕熼鍜佹綗闂傚倷绀侀幖顐﹀嫉椤掑嫭鍎庢い鏍ㄥ嚬閸ゆ洘銇勯幒鎴濐仾闁稿﹦鍏橀弻娑樷枎韫囷絾笑濠电偛鎲為崨顖滐紲闂佺粯鍔﹂崜娆戠矆閸愩劉鏀芥い鏂挎惈閳ь剚绻堥悰顕€宕奸妷銉庘晠鏌曟径濠冩崳闁哥姵鐗曢悾鐑筋敃閿曗偓缁€瀣亜閺冨洤浜归柛妯绘尦濮婂宕掑▎鎴濆闂佽鍠栭悥鐓庣暦濠靛棭鍚嬮柛銉e妼鎼村﹪姊洪崜鎻掍簴闁稿酣浜堕幏鎴︽偄閸濄儳顔曢梺鐟扮摠閻熴儵鎮炲ú顏呯厸濞达絿顭堥弳锝夋煛鐏炶濡奸柍瑙勫灴瀹曞崬顫滈崱姗堥獜濠碉紕鍋戦崐褏鎷归悢鐓庣闁瑰瓨绻嶅鏍ㄧ箾瀹割喕绨荤紒鐙€鍣i弻銈夊箒閹烘垵濮曢梺鍝勬婵炩偓婵﹥妞介獮鏍倷閹绘帩鐎虫繝鐢靛Л閸嬫捇鏌涘Δ鍐ㄢ偓锝夋晲婢跺﹦鐤€闂佸搫顦冲▔鏇㈩敊婵犲洦鈷戦柛婵嗗閳ь剚鎮傞獮鏍敃閿濆浂娲告俊銈忕到閸燁垶鎮¢妷锔剧瘈闂傚牊绋掗ˉ銏°亜鎼淬埄娈旈棁澶嬬節婵炴儳浜剧紓渚囧枟閻熲晛顕g拠娴嬫婵炲棙鍔曢崝鍛攽閻愭潙鐏﹂柨姘攽椤曞棛鐣垫慨濠冩そ瀹曨偊宕熼浣瑰缂傚倷绀侀鍡欐暜閿熺姷宓侀柛鈩冪☉缁秹鏌涢锝囩婵炵厧锕铏圭磼濡浚浜滆灒濠电姴鍋嗛悞鑺ユ叏濡灝鐓愰柍閿嬪笒闇夐柨婵嗘噺閸熺偤鏌熼姘卞ⅵ闁哄矉缍侀、妤呭焵椤掑嫬围缂佸娉曢弳锕€霉閸忓吋缍戦柛鎰ㄥ亾婵$偑鍊栭幐楣冨磻閻斿吋鍋╂繛宸簼閳锋垹绱撴担濮戭亪鎮橀崡鐐╂斀妞ゆ柨鎼埀顒佺箓閻g兘骞嬮悩顐壕闁挎繂楠搁弸鐔兼煟閹惧瓨绀冮柕鍥у楠炲洭鍩℃担鎻掍壕闁哄洢鍨归崙鐘绘煙鏉堥箖妾柣鎾存礀閳规垿鎮╅幓鎺濅患闂佸憡锚閻°劑骞堥妸锔剧瘈闁告洦鍘肩粭锟犳⒑閻熸澘妲婚柟鍐茬箻钘濋柣妤€鐗婇崕鐔哥節闂堟侗鐓繛宸墰缁辨捇宕掑顑藉亾閹间礁纾归柛婵勫劤閻挾鈧娲栧ú锕傤敃閼恒儲鍙忔慨妤€妫楁晶濠氭煕閵堝棙绀嬮柡灞炬礃缁绘繆绠涘☉娆樷偓宥囩磽閸屾氨孝婵炲樊鍙冨璇差吋婢跺﹣绱堕梺鍛婃处閸嬪懎鈻撻懜鐢电瘈闁靛骏绲剧涵楣冩倵濮橆厽绶叉い顐㈢箻閹粌螣娓氼垰娈兼繝鐢靛仜濡瑩宕归悽绋挎槬鐎光偓閸曨兘鎷哄┑鐐跺蔼椤曆勬櫠椤曗偓閺屾洟宕奸悢绋库偓鎰殽閻愬弶顥犲ù鐙呭閹叉挳鏁愰崱娆屽亾婵犳碍鈷戦悷娆忓閸斻倖銇勯弴銊ュ籍鐎规洏鍨藉畷锟犳倻閸℃ê鐦滈梻渚€娼ч悧鍡橆殽閹间胶宓佹俊銈呮噺閻撴洟鏌曟繛褍瀚В鍫ユ倵濞堝灝鏋ゆい顓炵墦閸┿儲寰勬繝搴㈠兊闁哄鐗冮弲顏嗘閹绘巻鏀介柣鎰摠鐏忎即鏌ょ憴鍕姢閻撱倝鏌曢崼婵囧櫝闁哄绉堕埀顒€绠嶉崕鍗炍涘▎鎾崇煑闊洦鎸撮弨浠嬫煟濡绲绘い蹇e亰閹粙顢涘☉姘垱闂佸搫鐬奸崰搴ㄦ偩閿熺姵鍋嬮柛顐g箖閻e姊绘担鍛婅础闁告鍛濠电姴娲ょ粻鏍煟閹达絾顥夌紒鐘劜閵囧嫰寮撮悙鏉戞婵炲濮寸紞濠傤潖婵犳艾纾兼慨姗嗗厴閸嬫挻顦版惔锝囩劶婵炴挻鍩冮崑鎾搭殽閻愬澧垫い銏℃礋婵″爼宕卞鍓х梾濠碉紕鍋戦崐鏍礉瑜忕划濠氬箣閻樼數鐒兼繝銏e煐閸旀牠鎮″▎鎾崇骇闁割偆鍠庨崝銈嗐亜閳哄﹤澧伴柍褜鍓濋~澶愬箰妞嬪孩顐芥慨妯挎硾閽冪喖鏌嶉妷锕€澧柛姘儔楠炴牜鍒掗崗澶婁壕闁告劕妯婇崝鈧梻鍌氬€峰ù鍥ь浖閵娧呯焼濞撴埃鍋撶€规洦鍨堕獮姗€顢欓懝鐗堟啺闂備礁鎼ú銏ゅ垂瑜版帗鐓侀柛銉e妿缁♀偓闂傚倸鐗婄粙鎺旂矈閳哄倷绻嗘い鎰暱閸嬫捇寮妷锔芥澑闂備胶绮崝妯间焊濞嗘劖娅犳繛鎴炵懅缁♀偓闂侀潧绻嗗Σ鍕嚀閸ф鐓曢柍鍝勫暙娴犺鲸顨ラ悙宸剶闁诡喗鐟╅幊鐘活敆閸屾稓鈧噣姊婚崒姘偓鐑芥嚄閸洍鈧箓宕奸妷锔芥珖闂侀潧顦崕宥吤洪鍛簻闂佸吋绁撮弲娑氱矈閿旂晫绡€闁汇垽娼у瓭闂佺娅曢崝娆撳箖閸ф鐒垫い鎺嗗亾闁宠鍨块幃娆撳级閹寸姳妗撴俊鐐€ら崢鐓幟洪鐐垫殾闁靛繈鍊栭悞鑲┾偓骞垮劚濡矂骞忓ú顏呪拺闂傚牃鏅涢惁婊堟煕濡亽鍋㈢€规洘绻勯埀顒婄秵閸犳鎮¢弴銏$厪闁割偅绻冮ˉ娆徝瑰┃鍨伈闁哄本娲熷畷鍫曞Ω閵夈儺娼氭俊銈囧Х閸嬬偟鏁敓鐘靛祦婵☆垰鐨烽崑鎾斥槈濞嗘鍔烽悷婊呭閹倸顫忔繝姘<婵炲棙鍩堝Σ顕€姊虹憴鍕偞闁告挻绻勭划顓㈡偄閼茬儤妫冨畷銊╊敇閻橀潧鐐婇梻鍌欑閹碱偆绮欐笟鈧畷銏ゆ偂楠烆啫鍥ц摕闁靛濡囬崢鍗烆渻閵堝棗濮夊┑顔芥尦瀹曟繂顭ㄩ崼鐔哄帗闂備礁鐏濋鍛存倶閹绢喗鐓涢悘鐐插⒔閳藉鏌嶇憴鍕伌鐎规洜鍠栭、鏇㈠閻欌偓濞兼盯姊婚崒娆戭槮闁圭⒈鍋婇、鏍幢濡炪垺鐩畷姗€顢欓懝鐗堟啺婵犵數鍋為崹鍫曞春閸愵喖纾婚柟鍓х帛閺呮煡骞栫划鍏夊亾閹颁焦浜ら梻鍌欑閹碱偊顢栭崱妤婃綎閻熸瑥瀚埞宥呪攽閻樺弶鎼愰柣顓燁殔椤法鎹勯悮鏉戜紣濡炪値鍋呯敮鎺曠亙闂佺粯锕㈠褎绂掗敃鍌涘仺妞ゆ牗銇涢崑鎾诲箛娴e憡顓挎俊鐐€栧ú宥夊磻閹剧粯鐓曢柍瑙勫劤娴滅偓淇婇悙顏勨偓鏍暜閹烘纾归柣銏㈩焾绾惧鏌熼悙顒€澧繛灏栨櫆閵囧嫰骞樼捄杞扮捕闂佸湱鏅弫璇差潖濞差亜浼犻柛鏇ㄥ幘娴煎洭姊洪崫銉バi柟鍛婂劤鍗遍柟鐗堟緲缁犳娊鏌熼崘鑼紞闁哥姵鐗曢悾鐑筋敃閿曗偓缁€瀣亜閹烘垵鈧粯鏅ラ梻鍌氬€搁崐鎼佸磹閻戣姤鍤勯柛顐f磵閳ь剨绠撳畷濂稿Ψ椤旇姤娅堥梻浣虹《閸撴繄绮欓幋鐘典笉濞寸厧鐡ㄩ悡鐘测攽椤旇棄濮囬柍褜鍓氶悧鏇㈡偩閻戣棄鐭楀璺虹灱閻﹀牓姊婚崒姘卞缂佸甯¢弫宥咁吋閸℃瑧顔曢柣蹇撶箲閻楁鈻嶉崱娑欑厪闁搞儜鍐句純濡ょ姷鍋炵敮锟犵嵁鐎n亖鏀介柛鎰╁妺婢规洟姊洪崨濠勨槈闁挎洏鍎靛畷锝堢疀濞戞瑧鍙嗛梺鍝勫暊閸嬫捇鏌涢妸锔剧畼闁瑰箍鍨藉畷鍗炩槈濞嗘垵骞楅梻浣筋潐濠㈡﹢宕ラ埀顒傜磼閵娿儺鐓奸柡灞界Х椤т線鏌涢幘鏉戝摵闁诡啫鍐剧叆闁割偅绻冮悗顒€顪冮妶鍡樷拻闁哄拋鍋嗗褔鍩€椤掑嫭鈷戦柛娑橈攻婢跺嫰鏌涘鈧粻鏍箖閻愬搫绀傞柤娴嬫櫇椤旀洟姊洪崷顓炰壕婵炲吋鐟╅幃鐐躲亹閹烘挾鍘遍柣搴秵閸嬪懐浜搁悽鍛婄厓鐟滄粓宕滃┑瀣剁稏濠㈣泛鈯曢崫鍕电叆闁割偅绻冮悗顒佺節閻㈤潧校闁告繂閰i崺鈧い鎴f硶椤︼箓鎽堕弽顓熺厱婵炴垵宕獮妯汇亜閿旇姤绶叉い顏勫暣婵″爼宕卞Δ鍐噯闂備胶顭堥敃銉╁箖閸岀偞鍋樻い鏇楀亾鐎规洖銈告俊鐑芥晜鐟欏嫬顏烘繝鐢靛仩閹活亞寰婇崸妤佸仱闁哄倹顑欓悞浠嬫煙闁箑鏋撻柛瀣尵閹叉挳宕熼鍌ゆО闂備焦瀵у畝鎼佸蓟瀹ュ洨纾兼俊顖濆吹閸欏棝姊虹€圭姵顥夋い锕€鐏氶幈銊╁焵椤掑嫭鐓熸俊顖濐嚙缁茬粯绻涢崼娑樷偓婵嗩潖濞差亝鍋¢柡澶嬪閸婎垶姊虹拠鈥崇仩闁兼椿鍨堕垾锕傚炊椤掆偓缁犱即骞栨潏鍓хУ婵炶尙顭堥埞鎴︽偐鐠囇冧紣闂佺粯顨呴敃顏堝箖閳ユ枼妲堥柕蹇ョ磿閸橀亶姊洪棃娑辨闂傚嫬瀚板鎼佸礋椤撶姷锛滈梺闈浤涢崟顒傚涧缂傚倷娴囨ご鍝ユ暜濡も偓椤曘儵宕熼瀣枛閹粌螣闂傚瓨鍠氭繝纰夌磿閸嬫垿宕愰幋锕€绀夊┑鐘叉搐绾惧潡鏌i姀銏╃劸缂佺姵鐗楃换娑㈠幢濡纰嶉梺钘夊暟閸犳牠寮婚弴鐔风窞闁割偅绻傛慨搴ㄦ⒑閸涘﹦鎳冮柨鏇ㄤ簻椤繒绱掑Ο璇差€撻梺缁樺灦閿氭繛鍫濈灱缁辨帡宕滆濡炬悂鏌涘▎蹇撴殭闁伙絿鍏橀獮瀣晝閳ь剙娲块梻浣虹《閸撴繂煤濠婂懐涓嶆慨妯垮煐閳锋垹绱撴担濮戭亪鎮樻潏銊ょ箚妞ゆ劑鍨归鈺呮煛娓氬洤娅嶆慨濠勭帛缁楃喖鍩€椤掆偓椤洩顦归柟顔ㄥ洤骞㈡俊鐐存礃濡炶姤淇婇幖浣肝ㄩ柕蹇ョ磿娴滄瑩姊绘担渚綊闁告洖鐏氶悾鐑芥⒑閹惰姤鏁遍悽顖ょ節瀵鈽夊顐e媰闂佺顫夐崝鏇⑺夊┑瀣拺闂侇偆鍋涢懟顖涙櫠娴煎瓨鐓曢煫鍥ㄦ閼版寧顨ラ悙鎻掓殻闁诡喗鐟╅幃婊兾熺紒妯煎絿闂傚倷鑳堕…鍫ュ嫉椤掆偓椤繈濡搁埡鍌涙珫闂佺粯鏌ㄩ崥瀣磹閻㈠憡鍋℃繛鍡楃箰椤忣亞绱掗埀顒勫焵椤掆偓閳规垿鎮欐0婵嗘疂缂備胶濮甸崹鍧楀箖妤e啯鍊婚柦妯侯槺閻撴垶绻濋姀锝嗙【妞わ箒浜划璇差潩閼哥鎷洪梻鍌氱墛缁嬫挻鏅堕弴銏$厵闁告劘灏欑粻鎶芥煃瑜滈崜姘舵嚌妤e啫绠犻柟閭﹀枟椤洟鏌熼悙顒€澧柛姘儔閺屾盯鍩勯崘顏呭櫑闂佹剚浜為幊鎾烩€旈崘顔嘉ч幖绮光偓宕囶啇婵犵數鍋熼妴瀣崲濠靛宓佸┑鐘插亞閻撱儵鏌涢銈呮珡婵☆偄鍟埞鎴︽倷閺夋垹浠搁梺鎸庢磵閺呮盯鈥﹂崶顒€绫嶉柛顐ゅ暱閹风粯绻涙潏鍓у埌闁硅绻濋獮鍡涘醇閵夛妇鍘甸悗鐟板閸嬪﹪宕曢弮鍌楀亾鐟欏嫭绀冪紒顔芥崌楠炲啴濮€閵堝懐顦ч梺缁樻尭缁ㄨ偐鑺遍崹顐$箚闁绘劦浜滈埀顒佺墵瀹曟繆顦寸紒顔碱煼楠炲鏁傞挊澶嗗亾瀹勬壋鏀介柣妯哄级婢跺嫰鏌i幘宕囩闁宠鍨块幃娆撳箣閺傚じ澹曢梻浣侯焾椤戝棝骞愰幖浣哥厴闁硅揪瀵岄弫濠囨煕韫囨洖甯堕柡瀣Т閳规垿顢欑涵閿嬫暰濠碉紕鍋樼划娆撴偘椤旇姤鍎熼柕濠忕畱濞堢喖姊洪棃娑辨闂傚嫬瀚埢鎾诲箹娴e厜鎷绘繛杈剧秬椤宕戦悩缁樼厱闁哄倽鍎荤€氱増銇勯鐐村枠闁轰焦鎹囬幃鈺呮濞戞哎鍋婇梻鍌欑閹诧繝宕濋敃鍌氬偍閻熸瑥瀚々鑼喐閻楀牆绗氶柣鎾寸懇閺岋綁骞嬮悘娲讳邯閹﹢鍩¢崨顔惧幈婵犵數濮寸€氼剚绂掓潏銊﹀弿濠电姴鍟妵婵囶殽閻愭潙濮堥柟顖涙閺佹劙宕堕埡鍌涱啌闂傚倸鍊烽懗鍫曗€﹂崼銉︽櫇闁靛牆顦粻鐔兼煥濞戞ê顏柣顓烆槺閳ь剙绠嶉崕閬嵥囬婊呯焼闁割偁鍨洪崰鎰熆閼搁潧濮囩痪鎯ь煼閺岀喖骞戦幇顒傚帿闂佸摜濮村Λ婵嬪蓟濞戙垹鍗抽柕濞垮劚椤偄顪冮妶蹇氱闁稿酣浜堕崺鐐哄箣閿旇棄鈧兘鎮规ウ鎸庮仩婵絻鍨虹换婵嬫偨闂堟稐姹楅梺绋款儐閹瑰洭骞冨Δ鍐╁枂闁告洦鍓涢ˇ銊╂⒑閹肩偛濡兼繛纭风節閹即顢欑喊杈ㄥ缓闂侀€炲苯澧存鐐诧工椤劑宕奸悤浣诡棃婵犵數鍋為崹鍫曟嚌妤e啯鐓€闂侇剙绉甸埛鎺懨归敐鍫燁棄闁告艾缍婇弻娑㈡偐閼碱儷銏°亜椤忓嫬鏆f鐐村浮瀵噣宕掑鍛Ц婵犵數鍋犻幓顏嗙礊閳ь剚绻涢崪鍐偧缂侇喖鐗婄换婵嬪磼濡や焦鏉搁梻浣虹帛閿氱€殿喖鐖奸獮鏍箛閻楀牏鍘搁柣搴岛閺呮繄绮i弮鍫熺厸鐎光偓閳ь剟宕伴弽顓炶摕闁搞儺鍓氶弲婵嬫煃瑜滈崜鐔兼偘椤曗偓瀵粙顢曢妶鍥风床闂備礁鎲¢幐椋庣矆娴e湱顩烽梺顒€绉甸悡娆愩亜閺冨倻鎽傛繛鍫熺矒閺屸剝鎷呴悷鏉款潔闂佽鍨卞Λ鍐垂妤e啯鍤戞い鎺嶇劍濞咃箓姊绘担钘夊惞闁哥姵鍔楅崚鎺撴償閵忊剝鐝峰┑掳鍊曢幊搴g不閺嶎厽鐓曢悘鐐村劤閸ゎ剚绻涢崗鑲╁⒈缂佽鲸鎸婚幏鍛存嚃閳╁啫鐏﹂柛鎺戯躬楠炴﹢顢欓悾灞藉箞婵犵數鍋為崹鍫曟晝椤愩埄鍟呴柕澶嗘櫆閻撴盯鏌涢埄鍐炬畼濠⒀嶇畵閺屸€崇暆鐎n剛袦婵犳鍠掗崑鎾绘⒑鐎圭姵銆冮柤瀹犲煐缁傛帡顢橀悜鍡樺瘜闂侀潧鐗嗛崯顐d繆婵傚憡鐓熸俊銈勭劍鐏忣厽銇勯弴顏嗙М妞ゃ垺娲熼弫鍌滅磼濡粯鐝ㄩ梻鍌欑窔閳ь剛鍋涢懟顖涙櫠鐎电硶鍋撶憴鍕妞ゎ偄顦垫俊鍫曟晲婢跺﹦顦ㄩ梺闈浤涢崨顔界帆濠电姷鏁搁崑鐘诲箵椤忓棗绶ら柦妯侯檧閼板潡寮堕崼姘珖闁活厽鐟ラ湁闁挎繂鐗婇鐘电棯閸欍儳鐭欓柡灞剧〒娴狅箓骞戦幇顒夋闂備線鈧偛鑻晶浼存煕韫囨棑鑰挎鐐插暣閹瑩鎮滃Ο缁樼彇濠电偠鎻紞鈧い顐㈩樀瀹曟娊鏌ㄧ€n剛鐦堥梺姹囧灲濞佳勭墡婵$偑鍊栧褰掓偋閻樿尙鏆︾憸鐗堝笚閻掕偐鈧箍鍎遍幊鎰邦敊閸ヮ剚鈷戦悷娆忓閸旇埖淇婇銏狀伃闁归攱鍨块幃銏ゅ传閵壯屽晭闂備胶鎳撻顓㈠磹閹存繍娼╂い鎴旀櫔缂嶄礁鐣锋總鍛婂亜缂佸鐏濇导搴㈢節瀵伴攱婢橀埀顒佸姍瀹曟垿骞樼紒妯煎幗濠德板€愰崑鎾绘煥閺囥劋绨绘い鏇秮椤㈡洟鏁愰崘銊ょ凹闂備礁鎲¢崝蹇涘棘娓氣偓楠炲繘鎼归崷顓狅紳婵炶揪绲芥竟濠囧磿韫囨稒鐓熼煫鍥ㄦ⒒缁犵偞銇勯姀鈽嗘疁濠殿喒鍋撻梺闈涚墕濡盯宕㈤悽鍛娾拺闁煎鍊曢弸鏂款熆瑜庨〃濠囩嵁閺嶎厼绠涙い鎾寸矆缁ㄨ顪冮妶鍡楀闁搞劏宕电划濠氭嚒閵堝倸浜鹃悷娆忓婢跺嫰鏌涚€n亷宸ラ柣锝呭槻閳规垹鈧綆浜為敍娆撴⒑缂佹ɑ鐓ュ鐟帮攻缁傛帡鍩¢崨顔规嫼閻熸粎澧楃敮鈺佄涢幋婵冩斀闁绘劏鏅涙禍鐐繆閵堝洤啸闁稿鍋ら獮鎴﹀炊椤掑倸绁﹂梺鍦劋椤ㄥ懐鐚惧澶嬬厵閻庢稒顭囩粻鏍ㄧ箾閸涱厾孝闁宠鍨块幃鈺佲枔閹稿孩顔囩紓鍌欐祰妞寸煤閻旈鏆﹂柟杈剧畱缁狅綁鏌ㄩ弴妤€浜剧紒鐐劤濠€閬嶅箟濮濆瞼鐤€闁哄洨鍋涢悘濠冪節閻㈤潧校闁肩懓澧界划濠氭晲閸℃瑧鐦堥梻鍌氱墛缁嬫挻鏅跺☉娆戠闁割偆鍠庨崝銈嗐亜椤忓嫬鏆e┑鈥崇埣瀹曞崬螖閸愵亝鍣梻浣筋嚙鐎涒晛顫濋妸鈺佺婵☆垯璀﹂崵鏇熴亜閹扳晛鈧劙宕戦幘缁樻櫜閹肩补鍓濋悘宥夋⒑缂佹ɑ灏紒缁樺姍閳ワ箓宕稿Δ浣告疂闂佹眹鍨婚。钘壩i崼婵愭富闁靛牆鍊瑰▍鎾绘煕閹惧銆掓俊鍙夊姍楠炴帒螖閳ь剟鎮¢姀銈嗙厓鐟滄粓宕滈悢椋庢殾闁硅揪绠戠粻鑽ょ磽娴i姘跺箯缂佹绠鹃弶鍫濆⒔閸掍即鏌熺拠褏绡€鐎规洦鍨堕幃娆撴倻濡厧骞堥梻浣告惈閸燁垶骞戦崶褜鐎舵い鏂垮⒔绾惧ジ鏌涚仦鐐殤閼叉牠姊洪崷顓熷殌閻庢凹鍘剧紓鎾寸鐎n偄鐧勬繝銏f硾閻吋顨欓梺璇叉唉椤煤濠婂牆绐楅柡宥庡幑閳ь兛绀侀埥澶娢熼柨瀣垫綌婵犳鍠楅敃鈺呭礈濞嗘垹涓嶆繛宸簼閳锋帒霉閿濆洤鍔嬮柛銈傚亾闂備礁鎲¢懝楣冾敄婢舵劗宓侀柛鈩冾殘閺嗗棝鏌涢弴銊ヤ簻闁诲寒鍙冮幃妤冩喆閸曨剛顦ュ┑鐐茬湴閸旀垿骞嗗畝鍕缂備焦菤閹峰姊洪崜鎻掍簽闁哥姵娲熼崺鈧い鎴f硶閻瑩鏌熼鎯у幋闁哄苯娲弫鍌炲箚瑜嶅Ч鏌ユ⒒閸屾瑧顦﹂柟娴嬪墲缁楃喎螖閸涱厼鍋嶉梺鍛婄箓鐎氣偓闁挎繂顦粻娑㈡煟濡も偓閻楀棝鍩€椤掑倹鏆柟顔煎槻閳诲氦绠涢幙鍐х棯缂備礁澧介崑鎾诲箖閸岀偛钃熸繛鎴欏灩鎯熼梺闈涱檧缁犳帞娑甸埀顒勬⒒娴e憡鍟為柣鐔村劦楠炲﹥鎯旈妸鈶╁亾閺冨牆绀冩い鏂挎瑜旈弻娑樷槈閸楃偟浠銈嗘煥濞差厼顫忛搹瑙勫厹闁告侗鍠氳ぐ褔姊洪崨濠冣拹闁荤喆鍎甸幃楣冩倻閽樺娼婇梺闈涚墕濡绂掑ú顏呪拺闁告稑锕﹂埥澶愭嚌瀹€鍕厵闂佸灝顑嗛妵婵囨叏婵犲懏顏犵紒杈ㄥ笒铻i悹鍥皺椤f煡姊虹拠鎻掝劉缂佸鐗撳鎻掆攽鐎n亞顔嗛悷婊呭鐢帡鎮橀幎鑺ョ厵濡娴囬崗宀勬煕閻愬灚鏆柟顔煎槻椤劑宕橀鐓庡強闂備線娼уΛ妤呭疮椤栨凹鍤楅柛鏇ㄥ灠缁犳稒銇勯幋鏃€娅旂紒鐘虫崌瀵鎮㈤崗鑲╁姺闂佹寧娲嶉崑鎾绘煟韫囨岸鍝哄ǎ鍥э躬楠炴捇骞掗幋鏃€瀵栫紓鍌欐祰妞存悂骞愭繝姘闁告侗鍠氶々鐑芥倵閿濆簼绨奸柟铏懇濮婂搫效閸パ呭姶闂佹悶鍔庨弲顐﹀箲閵忕姭鏀介悗锝庡墮缁侊附绻濋悽闈浶㈡繛璇х畵瀹曟垿骞囬鐘殿啎闂佽偐鈷堥崜娑氭暜濞戙垺鐓涢柛娑卞亜閻忓弶鎱ㄦ繝鍐┿仢闁哄苯鎳橀幃娆撴嚑鐠轰警浼冨┑鐘媰閸屾艾绁梺鍝勫閸撴繄绮悢鐓庣倞鐟滃酣鎮靛┑瀣€甸悷娆忓缁€鈧梺闈涚墢椤牓顢氶敐澶婄妞ゆ棁妫勬禍婊堟⒑閸涘﹦绠撻悗姘煎墰缁厼顫濋懜纰樻嫽婵炶揪缍€濡嫰宕ラ悷鎵虫斀妞ゆ棁鍋愰敍宥囩磼椤旇偐澧涢柟宄版嚇瀹曨偊宕熼崹顐%濠碉紕鍋戦崐鏍箰閸洖鍨傛繛宸簻绾炬寧淇婇妶鍕厡缂佺娀绠栭弻娑㈠焺閸忕媭浜濋幈銊╁磼濮n厾鎳撻…銊╁礋椤撶姷鍘滈梻浣告惈閺堫剙煤濠靛牏涓嶆繛鎴炵懅缁♀偓闂佺鏈崺鍐箯閵堝棔绻嗛柣鎰典簻閳ь剚鍨垮畷鏇㈡焼瀹ュ棗浜遍棅顐㈡处缁嬫垿鎮為崹顐犱簻闁圭儤鍨甸弸銈嗙箾閸忕厧濮堢紒缁樼洴瀹曪絾寰勭仦瑙f嫲濠电姷顣介埀顒€纾崺锝嗩殽閻愬澧柟宄版嚇瀹曨偊濡疯濮e洭姊婚崒娆戠獢婵炰匠鍛床闁割偁鍎辩壕褰掓煛閸モ晛鏋庢い鏇憾閺岋絽螣閼测晛绗¢梺缁樻尰濞茬喖寮婚敓鐘茬倞闁靛鍎遍‖鍫熺箾鐎涙鐭岄柛瀣仱婵$敻宕熼姘鳖啋闂佺粯鍔樺Λ鍕椤斿皷鏀芥い鏃傘€嬪銉︺亜椤撶偛妲婚柣锝囧厴楠炴帡骞嬮弮鈧悗濠氭⒑瑜版帒浜伴柛鐘虫崌瀹曟垵螣鐠佸磭绠氶梺缁樺姦娴滄粓鍩€椤掍胶澧柍缁樻閺佸啴宕掑顒傜崺婵$偑鍊曠换鎰偓姘间簼缁旂喖寮撮悙鈺傛杸闂佺粯鍔栧娆撴倶閿曞倹鍋ㄦい鏍ㄤ緱濞堟棃鏌嶇拠鑼х€规洖鐖奸崺锟犲礃椤忓海搴婂┑锛勫亼閸婃牕顫忔繝姘柧妞ゆ劧绠戠粻鐘绘煕閵夘喚鍘涙繛鍫滅矙閺岋綁骞囬鐔虹▏缂備焦顨嗙敮锟犲箺閸洖鍐€妞ゎ兘鈧磭绉洪柡浣瑰姍瀹曞ジ顢曢敐鍥┬ラ梻鍌欒兌缁垳缂撻崸妤€绀夐幖杈剧稻椤洟鏌熼幑鎰靛殭缁炬儳鍚嬮幈銊ヮ潨閸℃骞嬮梺绋款儐閹瑰洭鐛弽銊﹀闁告縿鍎荤槐顕€姊绘担铏瑰笡闁搞劌鍚嬮幈銊╁Χ婢跺﹦锛欓梺绉嗗嫷娈曢柣鎾卞劦閺岋繝宕堕埡浣风捕闂侀€炲苯澧柣鏍с偢瀹曟椽鍩€椤掍降浜滈柟鍝勬娴滈箖姊洪崫銉ユ瀾婵炲吋鐟╅幃楣冩倻閽樺顢呴梺缁樺姀閺呮粓鎮楁繝姘拺鐟滅増甯掓禍浼存煕濡湱鐭欐い銏$懇瀹曞爼濡歌閻﹀牓鎮楅崗绋垮祮闁衡偓閸楃儐鐔嗘慨妞诲亾闁糕斁鍋撳銈嗗笂閻掞妇绮堢€n偒娈介柣鎰嚋閺€濠氭煙椤栨稒顥堝┑顔瑰亾闂佸啿鎼崐褰掑汲閻愮儤鈷掗柛灞捐壘閳ь剚鎮傚畷鎰槹鎼达絿鐒兼繛鎾村焹閸嬫挻顨ラ悙宸█闁搞劌澧介幖鐐媴鐟欏嫨浠㈤梺杞扮閸熸潙鐣烽幒鎴僵妞ゆ帒鍊甸崑鎾活敇閵忊檧鎷洪梺鍛婄箓鐎氬嘲危瑜版帗鍊电紒妤佺☉濞层倕效閸欏绡€濠电姴鍊绘晶娑㈡煃闁垮娴柡灞剧〒娴狅箓宕滆閸n噣姊洪崨濠冪叆缂佸缍婇獮鍐ㄎ旈崘顏嗙暥濠电偞鍨堕敋妤犵偞锕㈤弻娑樷攽閸℃浼岄梺鍛婅壘椤戝懘鈥︾捄銊﹀磯闁绘碍娼欐慨娑㈡⒑閹稿海鈯曢柣鈺婂灠椤繐煤椤忓懎浠梺鍝勵槸缁ㄩ亶骞愰崘顏嗙=濞撴艾娲ゅ▍姗€鏌涢妸銉у煟妤犵偛鍟撮弫鎾绘偐閹绘帒绁梻浣虹帛濡礁鈻嶉敐澶嬪剨闁割偁鍎查埛鎺楁煕鐏炵偓鐨戝褎绋撶槐鎺斺偓锝庡亝鐏忎即鏌¢崨顓犲煟鐎殿喗鎸虫慨鈧柨娑樺楠炲牓姊绘担鍛婃儓闁稿﹤缍婇、鏍р枎閹惧磭锛熼梺鍝勫暙閻楀﹪鎮″☉姘e亾閸忓浜鹃梺閫炲苯澧寸€规洑鍗抽獮鍥敊閸撗呮殽闂備胶绮濠氬储瑜斿畷褰掑磼濞戞牔绨婚梺鍝勫暙閸婄敻骞忛敓鐘崇厽閹肩补妲呴崵鐔虹磼鏉堛劍宕岀€规洘甯掗埢搴ㄥ箳閹存繂鑵愮紓鍌氬€风欢锟犲闯椤曗偓瀹曞綊骞庨挊澶岊唹闂侀潧绻堥崐鏇㈡煁閸ャ劎绡€闂傚牊绋撴晶娑欑箾閸儳鐣烘慨濠冩そ瀹曠兘顢橀悙鎻掝瀱婵$偑鍊戦崝宀勫箠鎼粹埗娲锤濡や讲鎷绘繛杈剧秬椤宕戦悩缁樼厱閹兼番鍨婚惌鎺斺偓瑙勬礈閸犳牠銆侀弴銏″亜闁炬艾鍊搁ˉ姘繆閻愵亜鈧牠鎮у鍫濈;闁绘劕鎼悡鏇㈡煙鏉堥箖妾柛瀣剁秮閺屾盯濡烽幋婵嗘殶濡ょ姴娲娲传閵夈儰绮跺銈忕細閸楄櫕淇婇悽绋跨妞ゆ牭绲鹃弲婵嬫⒑闂堟稓绠氶柡鍛矌閻熝囨⒒娴h櫣甯涢柟绋跨埣瀹曟劙寮介妸褉鏀虫繝鐢靛Т濞村倿寮鍡樺弿婵妫楁晶顖炴煕婵犲骸鐏︽慨濠冩そ瀹曨偊宕熼澶嬶紒缂傚倷绶¢崰妤呭箲閸パ屽殨濠电姵纰嶉崑鍕煕韫囨洖甯堕柍褜鍓涚划顖炲箞閵娿儙鏃堝焵椤掆偓铻炴繛鍡樻尰閸嬧晠鏌涢锝嗙闁抽攱鍨圭槐鎾存媴閼测剝鍨规禍鎼佸箥椤斿墽锛滈柣鐘叉穿鐏忔瑦鏅堕敃鍌涚厽婵炴垵宕▍宥団偓娈垮枙缁瑩鍨鹃弽顓炍ㄩ柕澶嗘櫅瀵澘顪冮妶鍐ㄧ仾妞ゃ劌锕畷娲焵椤掍降浜滈柟鍝勭У椤﹂绱掔拠鍙夘棦闁哄被鍊曢湁閻庯綆鍋呴悵鏍磼閻愵剙鍔ら柕鍫熸倐瀵鏁愰崨顏呯€婚棅顐㈡处閺屻劌鈻嶈缁辨挻鎷呴崜鎻掑壍閻庤娲滈弫绋课i幇鏉跨闁哄啫鍊婚敍婊冣攽閳藉棗鐏ラ柛瀣姍閹潡宕熼鐔告杸闂佸疇妫勫Λ妤佺濠婂牊鐓曢柣鏇氱娴滀即鏌涢埞鍨姕鐎垫澘瀚换娑㈡倷椤掑倵鍋撶拠娴嬫斀闁绘劕寮堕ˉ鐐烘煕閵娿儳绉洪挊婵囥亜閺嶎偄浠﹂柍閿嬪浮閺屾稓浠﹂崜褎鍣紓浣疯兌婢ф濡甸崟顖氬嵆闁糕剝顨嗛崳鎶芥煕鐎n偅灏柍钘夘樀楠炴帡骞樼€电缍冨┑掳鍊楁慨鐑藉磻閻愬搫绀夋繛鍡楃箳閺嗭附淇婇娆掝劅闁哥喎鎳忛妵鍕籍閸屾稒鐝紓浣割儎缁€渚€鍩為幋锔藉亹闁割煈鍋呭В鍕節濞堝灝鏋ら柡浣割煼楠炲﹤鈹戠€n亞顦悷婊冪Ч钘熸慨妯垮煐閻撴洟鐓崶銊ㄥ濞存粌婀辩槐鎺楁偐閼姐倗鏆梺鍝勬湰閻╊垶宕洪崟顖氱闁绘瑢鍋撳ù婊勭箞楠炲牓濡搁敃鈧欢鐐烘煙闁箑骞橀柛姗嗕邯濮婃椽宕滈幓鎺嶇敖闂佸摜濮甸崝妤€鈻庨姀銈呯煑濠㈣泛鐗呯花璇差渻閵堝懐绠伴悗姘煎墴瀵娊鏁愰崨顏呮杸闂佺偨鍎辩壕顓㈠春閿濆洠鍋撶憴鍕鐎规洦鍓濋悘鎺旂磼閻愵剙顎滃瀛樼摃閳兘姊婚崒姘偓鎼佸磹閻戣姤鍤勯柛鎾茬閸ㄦ繃銇勯弽顐杭闁逞屽墮閸熸潙鐣锋總鍛婂亜缂佸鐏濇导搴ㄦ⒒娴e憡璐¢柧蹇撻叄瀹曟澘螖閸涱厾锛涢梺鍐叉惈閹冲繘鍩涢幋锔界厱妞ゎ厽鍨靛▍姗€鏌涙惔锛勭闁靛洤瀚板鎾綖椤撶喎鏋ら梻浣告惈婢跺洭宕滃┑鍡╁殫闁告洦鍘搁崑鎾绘晲鎼存繄鏁栨繛瀵稿У閹稿啿顫忓ú顏勪紶闁靛鍎伴弶顓㈡⒑閸涘﹥鐓ラ柣顓炲€块崹楣冨籍閸繄顦ㄥ銈嗘煥濡插牐顦归柡灞剧洴閸╁嫰宕楅悪鈧禍顏勵嚕閸愬弬鏃堝川椤旇瀚奸梻浣告啞缁哄潡宕曢崡鐐垫懃闂備浇顕х€涒晝绮欓崼銉ョ柧婵犻潧鐗嗛崹婵嬫倵閿濆簼鎲鹃柛姘儏椤潡鎳滈惉顏呭灴瀵煡顢楅崟顑芥嫼缂傚倷鐒﹂敋濠殿喖顦甸幃璺衡槈閺嵮冨Е濡ょ姷鍋涚换姗€骞栬ぐ鎺戞嵍妞ゆ挾濯寸槐鎶芥⒒娴d警鐒鹃柡鍫墴閹柉顦圭€规洘绻傞鍏煎緞鐎n亞褰呴梻鍌欑贰閸撴瑧绮旈悽绋跨9闁割偅娲滈崣鎾绘煕閵夆晩妫戦柛鎺斿椤ㄣ儵鎮欓幖顓熺暭缂備浇椴哥敮鐐垫閹烘嚦鐔虹箔鐞涒€充壕闁圭儤顨嗛悡鍐喐濠婂牆绀堟繛鎴欏灩閺嬩線鏌熼梻纾嬵唹闁逞屽墾缁犳挸鐣锋總绋课ㄩ柕澶堝劚娴滃爼姊虹拠鍙夋崳闁轰礁鎽滃☉鐢稿醇閺囩偟锛涢梺鍦亾閺嬪ジ寮搁弮鍫熺厱妞ゎ厽鍨甸弸鐔兼煟韫囨挾校缂佺粯绻堥幃浠嬫濞戞鎹曢梻浣瑰濞诧附绂嶅鍫晪闁挎繂顦介弫鍐煥閺囨浜剧紒鐐劤閵堟悂寮婚敐澶婄疀妞ゆ挾鍠撶粙鍥ㄧ箾鐎电孝闁靛牊鎮傞獮鍐ㄎ旈崨顓狀槯婵犮垼娉涢敃锝嗙珶閺囥垺鈷掑〒姘e亾闁逞屽墰閸嬫盯鎳熼娑欐珷闁圭虎鍠楅悡娆愩亜閺嶃劎鎳呯紒鎰⒒閳ь剝顫夊ú鏍Χ閸涘﹣绻嗛柣鎴eГ閺呮粓鎮峰▎蹇擃仼妞ゅ繑妞藉濠氬磼濞嗘帒鍘″銈庡幖閻楁挸顕i悽鍓叉晢闁逞屽墴閿濈偛鈹戠€n€晠鏌ㄩ弮鍥撻柣婵嗗槻閳规垿鎮欓弶鎴犱户闂佹悶鍔嶅浠嬪箖閿熺姴鍗抽柕蹇ョ磿閸樼敻姊绘笟鍥у伎缂佺姵鍨堕弲鑸电節濮橆厾鍘介梺鐟板⒔閹虫挻绂嶈ぐ鎺撶厓鐟滄粓宕滃┑瀣剁稏濠㈣泛鈯曢崫鍕庣喖宕楅悡搴$哎闂備礁澹婇崑渚€宕曟潏鈺冧笉闁哄稁鍘介悡蹇涚叓閸パ屽剰闁逞屽墯濞叉粎鍒掗崼銉ョ<闁绘劕顕崢鎯р攽閻愬瓨缍戞い鎴濇閳诲秹宕ㄩ鍛啍闂佺粯鍔栭幆灞解枔濠婂嫭鍙忓┑鐘插鐢稓绱掑Δ鍐ㄦ灈闁糕斁鍋撳銈嗗坊閸嬫挻銇勯鐐寸┛妞わ箑缍婇弻鐔碱敊閵娿儲鎼愭鐐灪缁绘盯骞嬮悜鍡欏姺闂佹寧绋掗悷鈺侇潖濞差亜宸濆┑鐘插濡插牓姊洪幐搴㈢┛缂佺姵鎹囨俊鎾川閺夋垹顔岄梺鐟扮畭閸斿秴螞閸愵喖鏋侀柟鐗堟緲瀹告繃銇勯幘璺烘瀾妞ゆ柨顦靛缁樻媴閻熸壋鏋欓梺琛″亾閺夊牃鏅滈弳婊堟煥閻斿搫孝闁藉啰鍠愮换娑㈠箣閻愮數鍙濆┑鐐茬焾娴滎亪寮诲☉銏犵婵°倐鍋撻悗姘煎墮閳诲秴螣鐠佸磭绠氶梺缁樺姦娴滄粓鍩€椤戭剙鎳忔刊濂告煥濠靛棙宸濆☉鎾崇Ч閺岀喖骞戦幇闈涙闂佽棄鍟伴崰鏍蓟閿濆妫橀柟绋垮閸庢捇姊洪崫鍕靛剰闁绘鎹囧璇测槈濡粍妫冨畷姗€濡搁妶鍥尲闂傚倷绀侀幗婊勬叏閹绢喗鏅濇い蹇撶墕缁犳牗淇婇妶鍛殲闁哥姴妫濋弻娑㈠即閵娿儱顫╁銈忚吂閺呯姴顫忓ú顏勭闁绘劖褰冮‖鍫ユ⒑缂佹澧柕鍫濇啞娣囧﹦鈧稒顭囬悷褰掓煃瑜滈崜娆擃敋閿濆绠绘い鏃傗拡濞煎﹪姊洪弬銉︽珔闁哥噥鍨堕幃鐢稿冀椤撶啿鎷绘繛鎾村焹閸嬫捇鏌嶈閸撴盯宕戝☉銏″殣妞ゆ牗绋掑▍鐘绘煛婢跺鍎ラ柣鏂挎閹嘲鈻庤箛鎿冧痪缂備讲鍋撻柛鎰典簽绾捐偐绱撴担璇$劷缂佺姵鎸婚妵鍕敃閿濆洨鐤勫銈冨灪閿曘垽骞冮埡鍛闁圭儤姊婚弶浠嬫⒒閸屾艾鈧悂宕愰悜鑺ュ€块柨鏇炲€搁崙鐘测攽閸屾粠鐒鹃柣銈囧亾缁绘盯骞嬪▎蹇曚患缂備焦鍔栭〃鍡涘箞閵娿儺娼ㄩ柛鈩冾殔婵箓姊虹紒妯烩拻闁告鍐惧晠婵犻潧顑嗛崐鍨箾閹寸偟鎳愰柣鎺嶇矙閺屾稑鈻庤箛鎿冧純濠碘槅鍋勯幊姗€銆侀弴銏狀潊闁炽儲鍓氬Σ閬嶆⒒娴g瓔娼愰柣鈩冩礀閻g兘鎮界粙璺唵閻熸粎澧楃敮妤呭疾閹间焦鐓熸俊顖濇閿涘秹鏌涘Ο鎸庮棄妞ゎ亜鍟存俊鍫曞幢濡儤娈梻浣告憸婵敻骞戦崶顒傚祦濠电姴娲ょ粈瀣亜閹捐泛啸闁挎稒绮庣槐鎾诲磼濞嗘垵濡藉銈庡幖濞层倗鍙呴柣搴f暩绾爼宕戦幘鑸靛枂闁告洦鍓涢ˇ銉╂倵鐟欏嫭澶勯柛鎾跺枛瀹曟椽濮€閳╁啫鍔呴梺闈涚墕濞层劑寮堕幖浣圭厵闁兼祴鏅炶棢濠碘剝褰冮幊搴ょ亱濠电姴锕ら悧濠囧煕閹烘嚚褰掓晲閸モ晜鎲橀梺鎼炲€栭悷鈺侇潖閾忚鏆滄い鏃€鍎抽崺灞筋渻閵堝骸骞栨繛娴嬫櫊钘濈憸鐗堝笚閻撴瑦銇勯弽銊︾殤闁绘帒鎽滈埀顒冾潐濞叉鏁幒妤嬬稏婵犻潧顑呯粈鍌炴煠濞村娅囬柍璇差槸閳规垿鎮╅崹顐f瘎闂佺顑嗙粙鎴g亽婵犵數濮撮崯浼淬€呴崣澶岀瘈闂傚牊绋撻幊浣割熆閼搁潧濮囬梺鍗炴喘閺岋綁寮崶顭戜哗濡炪倖姊瑰ú鐔奉潖濞差亝鍋¢梺顓ㄧ畱濞堝爼姊虹粙娆惧剳濠殿喚鏁哥划鈺呮偄閼茶櫣鍠庢晥闁搞儻濡囬惄搴ㄦ⒒娴g懓顕滅紒璇插€块獮濠呯疀濞戞鐣鹃梺鍓插亖閸庢煡鎮¢崘顔藉仭婵炲棗绻愰鈺呮煟韫囨梹灏﹂柡灞剧洴閸╃偤宕归鐓幮曢柣搴ゎ潐濞叉牕鐣烽鍕ㄢ偓鏃堝礃椤旇偐顦悷婊冪Ч瀹曠敻顢楅埀顒勫煘閹达附鏅柛鏇ㄥ亗閺夘參姊虹粙鍖℃敾闁搞劌鐏濋悾宄扳攽閸℃瑦娈曢梺鍛婃处閸撴瑦绂嶉柆宥嗩棅妞ゆ劑鍨烘径鍕磼鐎n偄鐏╃紒顔肩墦瀹曞崬鈽夊▎鎴濆箥闂備胶绮崹鍫曟晝閳轰讲鏋旈柕蹇嬪€栭悡娑樏归敐鍛暈闁哥姵锕㈤弻锛勪沪閻愵剛顦紓浣哄У閻╊垰顕i幘顔藉€烽柟鎵虫櫅閸旀粓鏌曢崶褍顏€殿噮鍓熷畷鐘诲灳閸忓懐鐭楅梻鍌欑閻ゅ洭锝炴径鎰瀭闁割偅娲滃畵浣糕攽閻樺弶澶勯柣鎾存礀閳规垿鎮╅幓鎺撴闁诲繐绻掗弫鍝ユ閹烘鏁婇柤娴嬫櫅椤も偓缂傚倷鐒﹂〃鍫ュ窗閺嶎厼鏄ラ柍褜鍓氶妵鍕箳閹存繍浠奸梺鍝勫閸庣敻寮诲鍫闂佸憡鎸诲畝鍛婁繆閻㈢绀嬫い鏍ㄦ皑椤斿﹪姊虹化鏇炲⒉闁靛洨鍋炵粩鐔煎即閵忊檧鎷绘繛杈剧悼閻℃棃宕靛▎鎴犵<缂備焦锚閻忋儵鏌i敐鍡欑疄妤犵偞鐗楅幏鍛村传閸曨厹鍋婇梻鍌欑婢瑰﹪宕戞笟鈧畷鏇熸綇閵娿儱濮呴梻鍌氬€风欢姘焽瑜旇棟妞ゆ牗顕㈣ぐ鎺撳€婚柦妯侯槺閻涖儵姊洪崫鍕枆闁告鍋愮划濠氬冀椤撶喓鍘撻梺瀹犳〃缁€渚€寮抽悙鐑樼厱閹艰揪绲介弸娑㈡煛鐏炵晫效濠碉紕鍏樻俊鎼佸Ψ瑜庨妤呮⒑濮瑰洤鐒洪柛銊ㄤ含缁瑩骞掗弮鈧畷鍙夌節闂堟侗鍎愰柛瀣ㄥ姂濮婂宕奸悢宄扮€┑鐐村灟閸ㄦ椽鎮″▎鎴斿亾閻熸澘顏繝銏★耿瀵娊鏁愰崶锝呬壕閻熸瑥瀚粈鍫ユ煕閻樺磭澧甸柕鍡曠窔瀵挳濮€閳哄倹娅囬梻浣瑰缁诲倻鈧稈鏅犺棢閻庯綆鍓涚壕浠嬫煕鐏炴崘澹橀柍褜鍓氶幃鍌氱暦閹邦剛鏆嬮柟鍐诧工缂嶅﹤鐣烽崼鏇炍╅柨婵嗗閻帡姊绘担鍛婂暈缂佸搫娼″畷鏇㈠蓟閵夈儲杈堝┑鐘诧工閻楀﹪鎮¢妷鈺傜厽闁哄倹瀵ч幆鍫㈡偖閵娾晜鈷戦梺顐ゅ仜閼活垶宕㈤崫銉х<闁逞屽墯缁楃喖鍩€椤掑嫬鏄ラ柕蹇婂墲閸庣喖鏌曟繛鍨姢妞ゆ挸鎼埞鎴︽偐缂佹ɑ閿┑鐐茬湴閸旀垿宕洪埀顒併亜閹哄秶顦﹂柍缁樻礋閺岋紕浠︾粙鍨拤閻庡灚婢樼€氼厾鎹㈠┑瀣妞ゆ劦鍋呭▓濂告⒒閸屾瑧顦﹂柟纰卞亰楠炲﹨绠涘☉娆忓壆濡炪倖鐗滈崑鐔风暤娓氣偓閺屾盯骞囬棃娑欑亪缂備胶濯寸紞渚€寮婚妸鈺佺睄闁稿本绋掗悵顏堟⒑閸涘⊕鑲╁垝濞嗘挸钃熼柣鏃傚帶缁€鍌炴煠濞村娅嗘繛鍫墴濮婅櫣鍖栭弴鐔哥彅闁诲孩纰嶅姗€鎮鹃悜绛嬫晬婵犻潧鐗忛弶绋库攽閻愭潙鐏﹂柣鐔濆洤鍌ㄩ梺顒€绉甸埛鎴犵磽娴e厜妫ㄦい蹇撴椤ユ碍銇勯幘璺烘瀾婵炲懐濞€閺岋綁濮€閻樺啿鏆堥梺缁樻尭閸熸挳寮婚弴鐔风窞婵☆垵娅f禒顖炴⒑娴兼瑧鎮奸柡浣割煼瀵鏁嶉崟顏呭媰闁荤姴娲﹁ぐ鍐€栫€n喗鈷戦梺顐ゅ仜閼活垱鏅堕崜褏纾奸柛娆忣槹閵囨繄鈧鍠楄ぐ鍐煘閹达箑閱囨い顐幘閻熸繃绻濆▓鍨灍妞ゎ厼鐗撳畷娲冀椤撶偟鍘遍梺鐟邦嚟婵澹曢挊澹濆綊鏁愰崪浣圭稑濡炪倕绻愰悧濠囧磹閸洘鐓曟俊銈呭暙娴滃綊鏌¢埀顒勬嚍閵夛絼绨婚梺鍝勫€圭€笛囧箚閸儲鐓冪憸婊堝礈濮樿鲸宕查柛宀€鍎愰弫瀣煥濠靛棭妲哥紒鐘垫暬閺岀喖鎮滃Ο鑲╃暭闂佸憡鐟ュΛ婵嗩潖濞差亜绀堥柟缁樺笂缁ㄤ粙姊洪崫銉バi柟鐟版搐閻g兘濮€閵堝棭妫冨┑鐐村灱妞村摜鈧潧鐭傚娲濞戞艾顣哄┑鈽嗗亝缁嬫帡寮查崼鏇ㄦ晜闁告侗鍓涚粻姘渻閵堝棗濮х紓宥呮閳绘挸顭ㄩ崨顏勪壕閻熸瑥瀚径鍕煕閵娿儳鍩i柕鍡曠窔瀵挳濮€閳╁啯鐝曢梺鑽ゅ仦缁嬪牓鍩€椤掆偓閸樻牗绔熼弴銏♀拺闁告稑锕﹂埊鏇㈡煙椤栨氨鐒哥€殿噮鍋婂畷鍗炩槈濞嗘垵骞堥梻浣告惈濞层垽宕濆畝鍕偍闁圭虎鍠楅悡娆戔偓鐟板閸嬪﹪鎮¢崗鍏煎弿濠电姴鎳忛鐘电磼椤旂晫鎳囨鐐村姈閹棃濮€閳ユ剚浼嗛梻鍌氬€烽懗鍫曞储瑜忕槐鐐寸節閸曨厺绗夐梺鍝勭▉閸樺ジ寮伴妷鈺傜厓鐟滄粓宕滃璺何﹂柛鏇ㄥ灠缁犲磭鈧箍鍎卞ú銈嗕繆娴犲鈷戠紒瀣皡閺€濠氭煕閺冣偓閻熲晛顕g拠宸悑濠㈣泛谩閵婏负浜滈柡宥冨妿閻矂鏌¢崱鎰偓鏇⑩€旈崘顔嘉ч柛鎰╁妿娴犳儳顪冮妶鍐ㄥ闁挎洏鍊濋幃楣冩倻閼恒儱浜滅紒鐐妞存悂寮插┑瀣拺闂傚牊绋撴晶鏇犵磼缂佹ê娴柣娑卞櫍婵偓闁靛牆妫岄幏濠氭⒑缁嬫寧婀伴柣鐔濆泚鍥晝閸屾稓鍘靛┑鐐存綑椤戝倿宕戦幘鑸垫儱濞达綀顫夐妵婵嬫煛娴g鏆g€规洘甯掗~婵嬪箟鐎n兛瑕嗛梻鍌欐祰椤曆囧礄閻e瞼绀婇柛鈩冪☉閻掑灚銇勯幋鐐插姢闁诲浚浜濇穱濠囨倷閹殿喚鐓撻梺闈涙缁舵艾顕i鈧畷鐓庘攽閸℃瑧宕哄┑锛勫亼閸婃牕顫忔繝姘柧妞ゆ劑鍎禍褰掓煕閵夘喖澧柍閿嬪浮閺屾稓浠﹂崜褎鍣紓浣瑰姈濡啴寮诲鍫闂佸憡鎸婚惄顖氱暦閹存績妲堥柕蹇娾偓铏吅婵$偑鍊栭悧妤冪矙閹烘垟鏋嶉柣妯款梿瑜版帗鍋傞幖杈剧稻閹插ジ姊虹紒妯诲鞍婵炲弶顭囬幑銏犫槈閵忕姴鑰垮┑掳鍊曢崯浼搭敊婢舵劖鈷戦柟鑲╁仜閳ь剚娲栫叅闁挎洖鍊哥粻鐐烘煏婵犲繐顩紒鈾€鍋撻梻浣告啞閸斿繘寮崒娑氼浄闁靛繈鍊栭崐鐢告偡濞嗗繐顏璺哄閺屾稓鈧綆浜峰銉╂煟閿濆洤鍘撮柟顔哄灮閸犲﹥娼忛妸锔界彎濠电姷鏁搁崑鐐哄垂閸洘鍋$憸鏃堝春閳ь剚銇勯幒鎴濐仹闁硅尙鍋撻幈銊︾節閸曨厼绗¢梺鐟板槻閹冲繒绮悢纰辨晬婵犲﹤鍟瓏缂傚倸鍊搁崐鐑芥嚄閸撲礁鍨濇い鏍仜閸ㄥ倿鏌涜椤ㄥ懘寮告笟鈧弻娑㈠箛闂堟稒鐏堝銈庡亜閹虫﹢寮婚敐鍛傜喖鎼归柅娑氶┏婵犵數鍋涢悧鎾剁不閺嵮屾綎婵炲樊浜滅粻浼村箹鏉堝墽鎮奸柣锝夋涧椤啴濡惰箛鎾舵В闂佹悶鍔岀壕顓㈠礆閹烘鍤掗柕鍫濇川閿涙粌鈹戦埥鍡楃仸闁哄懓灏欓懞杈ㄧ節濮橆厸鎷洪梺鍛婄箓鐎氼剟寮冲▎鎰濠㈣埖绋撻悾鍨殽閻愭潙绗掗摶鏍煃瑜滈崜娑氬垝婵犳凹鏁嶆慨姗堢稻閺傗偓闂備胶绮敋缁剧虎鍙冮妴鍌炲蓟閵夛妇鍘撻梻浣哥仢椤戝懘鎮橀埡鍐<閺夊牄鍔岀粭褔鏌嶈閸撱劎绱為崱娑樼;闁告洦鍨奸弫瀣節婵犲倸顏紒鈾€鍋撻梻渚€鈧偛鑻晶顖炴倵娴e啫浜归柍褜鍓氱粙鎺椻€﹂崶顒€鍌ㄥù鐘差儐閳锋垹绱撴担鑲℃垹绮堥埀顒勬⒑缁嬪尅鏀婚柟顔煎€挎俊鎾川閹碱厽鏅㈤梺绋挎湰缁酣鏁嶅鍐炬富闁靛牆妫欓埛鎺楁煏閸℃鍎旂€殿喓鍔嶇换婵嗩潩椤撶偐鍋撻棃娴㈠綊鏁愰崨顓熸婵炲瓨绮岀紞濠囧蓟瀹ュ牜妾ㄩ梺鍛婃尰濮樸劎鍒掑▎鎾崇婵$偟鍎甸崑鎾绘晝閸屾氨鍊炲銈嗗坊閸嬫捇鏌涚仦璇插闁靛洤瀚粻娑㈠箻鐠轰警鏉搁梻浣瑰▕閺€閬嶅垂閸︻厽顫曢柟鐑橆殢閺佸秵绻涢幋鐐垫噮闁挎稒娲熷铏圭矙濞嗘儳鍓遍梺鐟版啞閹倿骞冩ィ鍐╁€婚柦妯侯槺閸婄偤姊洪崘鍙夋儓闁挎洏鍊濆顐ゆ喆閸曨厾鐦堥梺姹囧灲濞佳勭濠婂牊鐓熼幒鎶藉礉鎼淬劌绀嗛柟鐑橆殔缁犲鏌涢幘鍙夘樂缂佹顦靛娲传閸曨喚妾ㄩ柣蹇曞仜婢х晫绮欐担铏圭=闁稿本鑹鹃埀顒傚厴閹偤鏁冩担瑙勫櫡婵犵數濮甸鏍垂閸楃儐鐒芥繛鍡樻尭杩濋梺鍦劋閸╁牆顭囬埡鍛厽闁规崘娅曢幑锝吤归悪鈧崹璺侯潖濞差亜宸濆┑鐘插暊閹疯顪冮妶搴″箹闁绘鎹囬崹楣冨籍閸繄顦ㄥ銈嗘煥濡插牐顦归柡灞剧洴閸╁嫰宕橀悙顒傛毉濠电偛顕慨闈涱焽濞嗘挸鐓橀柟杈剧畱閻擄繝鏌涢埄鍐︿沪缂併劏鍋愮槐鎾存媴缁涘娈梺缁橆殕閹瑰洭鐛崘鈺侇嚤闁圭⒈鍘介弲顏堟⒑闁偛鑻晶鎾煟濞戝崬娅嶇€规洖鐖奸、妤呭焵椤掑倻妫憸鏃堝箖鐟欏嫮鐟规い鏍ㄧ矊鐢儵姊洪崫銉ユ瀻婵炲眰鍊濋崺鐐哄箣閿旇棄鈧兘鏌ら幖浣规锭婵炴嚪鍛=濞达綀妫勯拕鍏间繆椤愩垹顏柡浣稿暣婵偓闁靛牆妫涢崝鍫曟倵楠炲灝鍔氭俊顐n殕缁傛帗绺介崨濞炬嫼闁荤喐鐟ョ€氼剟宕濈捄琛℃斀妞ゆ柨鎼埀顒佺箞瀹曞搫鈽夐姀鐘殿唺濠德板€撻懗鍫曞储闁秵鐓熼煫鍥ㄦ礀娴犳粌顭胯缁瑩鐛繝鍥у耿婵炴垶鐟ч崢閬嶆椤愩垺澶勯柟鎼佺畺閹ɑ娼忛埡鍐紲闁哄鐗勯崝灞矫归濮愪簻闁靛繆鈧啿鎽甸悗瑙勬磸閸旀垿銆佸鈧幃鈺傛綇椤垶鏅i梻鍌氬€搁崐宄懊归崶褜娴栭柕濞у懐鐒兼繛鎾村焹閸嬫挻銇勯姀锛勫⒌鐎规洏鍔戝鍫曞箣閻樻彃绠i梻鍌欒兌椤㈠﹪骞撻鍡欎笉闁硅揪闄勯崑鍌炴煥閻斿搫校闁绘挻娲熼弻宥夊煛娴e憡鐏撳┑鐐茬墛閿氶棁澶愭煟濮楀棗浜濇繛鍛攻閹便劍绻濋崘鈹夸虎濡ょ姷鍋為崝鏍箚閺冨牆顫呴柣娆屽亾婵℃彃宕埞鎴︽倷閼碱剚鎲肩紓渚囧枛缁夊爼宕氶幒妤€绠婚悹鍥皺閻g儤淇婇妶蹇曞埌闁哥噥鍨跺畷鎰節濮橆厾鍙冨┑鈽嗗灟鐠€锕€危閸濄儮鍋撶憴鍕碍婵☆偅绻傞~蹇撁洪鍜佹濠电偞鍨跺銊╊敊婵犲啰绡€婵炲牆鐏濋弸銈夋煕韫囨棑鑰挎鐐插暣瀹曠螖閳ь剟鎮為崹顐犱簻闁圭儤鍨甸顏堟煃闁垮绗掗棁澶愭煥濠靛棛澧涙い蹇曞█閹粙顢涘☉姘e闂侀潧娲ょ€氱増淇婇幖浣肝ㄩ柨鏇楀亾婵炲牊顨婂铏规嫚閳ヨ櫕娈梺绯曞墲閻熝囧级缁嬪簱鏀介柣鎰綑閻忥箓鏌ㄥ鑸电厱閻庯綆浜炴晥闂佸搫澶囬崜婵嗩嚗閸曨剛绡€闁告洦鍋掗弳銉╂⒒娴e憡鍟為柡灞诲妼闇夌€瑰嫰鍋婇崵鏇犳喐閺冨牆鏄ラ柍褜鍓氶妵鍕箳閹存繍浠鹃梺鎶芥敱閸ㄥ爼骞堥妸鈺傚仭闁绘鐗婇幃娆撴⒑鐠囪尙绠扮€殿喖澧庨幑銏犫槈濞嗘劕顎撻梺鍛婂姈瑜板啴寮抽悢鍏肩厵濠殿喗鍔曢崝锔芥叏婵犲嫮甯涢柟宄版噽缁數鈧綆浜濋鍕⒑鐠囨彃顒㈢紒瀣墦瀵煡鎮╅懠顒佹濠电偛妫欑敮鍥ㄧ瑜版帗鐓欓柣鎴灻悘鈺呮煟閹炬潙鐏存慨濠冩そ瀹曘劍绻濋崒姣挎洟姊虹紒妯诲碍闁绘鎸搁悾鐑芥偨缁嬪灝宓嗛梺闈涢獜缁辨洟宕㈤悽鍛娾拺闁告稑锕ョ亸顐︽煠閸愯尙鍩f鐐搭殜瀹曟帡鎮欑€电骞愬┑鐐舵彧缁蹭粙骞夐敓鐘撳濮€閵堝棛鍘搁柣蹇曞仜婢ц棄煤鐎电硶鍋撳▓鍨灍闁规瓕娅曟穱濠囧箹娴h倽銊╂煏婢舵ê鏋熷Δ鐘插濮婂宕掑▎鎴М闂佸湱瀵介妶鍡樺櫡闂傚倷娴囬鏍窗閺嶎厼纾归柛顭戝櫘閸ゆ洖鈹戦悩宕囶暡闁哄懏鐓¢弻娑㈩敃閻樿尙浼勯梺鍝勵槹閹倸顫忓ú顏勪紶闁告洦鍓欑粣娑㈡⒑缁嬫鍎愰柨鏇樺灩閻g兘顢曢埗鑺ユ閸┾偓妞ゆ帒瀚ч埀顒佹瀹曟﹢顢欓崲澹洦鐓曢柍鈺佸枤閻掗箖鏌涚€b晝绐旀慨濠冩そ瀹曘劍绻濋崘顭戞П濠电偛鐡ㄧ划搴ㄥ磻閻斿搫鍨濋悹鍥ф▕濞尖晜銇勯幘璺盒ラ柣锕€鐗撳濠氬磼濮樺崬顤€缂備礁顑嗛崹鍧楀春閳ь剚銇勯幒宥囧妽闁稿﹥鍔栭〃銉╂倷瀹割喗鈻堥梺杞扮劍閹瑰洭骞冮埡鍛闂婎偒鍘鹃弳妤呮⒒閸屾瑧顦﹂柟璇х節瀹曟繈鏁冮崒姘辩崶濠德板€曢幊搴e婵犳碍鐓冮柍杞扮閺嗙喓绱掗悩鑽ょ暫闁哄本鐩崺鍕礃閻愵剛鏆紓鍌欒兌婵攱鏅跺Δ鍛﹂柛鏇ㄥ枤閻も偓婵犵數濮撮崯顖炴偟濮樿埖鈷戦柛婵嗗閻掕法绱撳浣镐壕缂傚倷鑳舵慨鐢告儎椤栫偟宓佹繛鍡樻尭缁€鍐煏婵犲繐鐦滈柛鐔插亾闂傚倸鍊搁崐椋庢濮樿泛鐒垫い鎺戝€告禒婊堟煠濞茶鐏¢柡鍛埣瀹曪絾寰勯崼婊呯泿婵$偑鍊栭崝鎴﹀春閸曨倠锝夊箹娴g懓浜楅梺闈涚墕椤︿即鎮″☉姘e亾鐟欏嫭鎯勯柛鐘崇墵楠炲﹨绠涢幘顖涚亖闂佽鍨庣仦鎯х槣闂備線娼ч悧鍡椢涘Δ鍐當闁圭儤顨嗛崐鍨叏濡厧甯跺褎鎸抽弻鐔碱敋閸℃瑧鐦堥梺鎼炲姂缁犳牠鐛崶銊﹀闁告繂瀚弳鈺呮⒒閸屾瑧顦﹂柛姘儔楠炲啴宕掑鑲╁姺閻熸粌閰i獮鍫ュΩ閳轰胶鍊為梺鍐叉惈閸熶即鏁嶅鍫熲拺缂備焦锕笟娑㈡煕閻樺磭澧电€规洘绻傞~婵嬫嚋濞堟寧鈷栧┑鐘灱閸╂牠宕濋弽顓熷亗闁靛濡囩弧鈧梻鍌氱墛缁嬫帡鏁嶅鍡曠箚闁煎ジ顤傚鎰磼缂佹娲寸€规洏鍔戦、娆撳礈瑜忛崢鎰繆閻愵亜鈧倝宕i埀顒佺箾婢跺绀嬫鐐差樀楠炴﹢顢欓懖鈺婃Ч婵$偑鍊栫敮鎺楀磻閸℃あ锝夘敆閸曨兘鎷绘繛杈剧到閹芥粓寮搁崘鈹夸簻妞ゆ劑鍩勫Ο鈧悗瑙勬礀缂嶅﹤鐣锋總绋垮嵆闁绘灏欓妶锕€鈹戦悩鍨毄濠殿喗娼欑叅闁挎洖鍊归崑鍌炴煛閸モ晛浜归柡鈧禒瀣厽婵☆垵顕х徊濠氭煛閸℃鎳冮柍瑙勫灴椤㈡瑩鎳栭埞顑惧€濋弻宥堫檨闁告挻绻堥敐鐐村緞婵炴帒鎼~婊堝焵椤掆偓閻g柉銇愰幒鎴︽暅濠德板€曢崯顐ょ矈閿曗偓閳规垿鍩ラ崱妤冧淮闂佺顑嗛崝妤佺珶閺囥垹绀傞柛蹇曞帶瀵灝鈹戞幊閸婃劙宕戦幘缈犵箚妞ゆ劧绲块幊鍥煕閳哄倻娲寸€殿喖鈧噥妲烽梺琛″亾濞寸姴顑嗛悡鐔告叏濡も偓濡寮稿☉銏$厽闊洦宀搁崫铏圭磼缂佹鈯曠€垫澘瀚埀顒婄秵閸撴岸宕氬☉姗嗘富闁靛牆鍟悘顏堟煟濡ゅ啫孝闁伙絿鍏樺畷濂稿即閻愰潧骞愬┑鐐舵彧缁查箖宕濋崨顓ф僵闁煎摜顣介幏娲⒒娓氬洤浜為柛瀣洴閹崇喖顢涘☉娆愮彿濡炪倖鐗楃划搴e閼测晝纾藉ù锝堫嚃閻掔晫绱掗悩闈涗槐闁哄瞼鍠栭、娆撴嚒閵堝洨鍘繝纰樻閸嬪嫰宕锔界畳闂傚倸顭崜姘炽亹閸愵喗鍊堕柡灞诲劜閻撴盯鎮橀悙鎻掆挃闁愁垱娲滅槐鎺旂磼濡偐鐤勯悗瑙勬礃鐢帡鈥﹂妸鈺佸窛闁告侗鍋勬慨鍌炴煛瀹€瀣暠閾伙綁鏌i幘鍐差劉闁诲骸澧界槐鎾存媴閾忕懓绗$紓浣筋嚙閸熶即骞戦姀鐘斀閻庯綆浜為敍婊冣攽閻愭潙鐏﹂拑杈ㄣ亜韫囥儳绡€婵﹦绮幏鍛瑹椤栨粌濮兼俊鐐€栭崹闈浳涘┑瀣畺鐟滃秷鐏冮梺鍛婁緱閸橀箖鎮块崟顖涒拺闂傚牊渚楅悞楣冩煕鎼粹剝鎯堟い顓炴喘婵℃悂鍩¢崒婊冨箞闂備焦鏋奸弲娑㈠窗濮橆兘鏋旈柡鍐ㄥ€荤壕濂告煟濡儤鎯堥柛姘贡缁辨帗娼忛妸锕€闉嶉梺鐟板槻閹虫ê鐣烽锕€绀嬮柕濠忓閳ь剚澹嗙槐鎾诲磼濞嗘帒鍘℃繝娈垮枤閺佸骞冭閹晛顔忛鍏碱吙濠电姷鏁告慨鐢告嚌閻愵剙鍔旈梻鍌欑窔濞佳囁囬銏犲瀭婵炲樊浜滃Λ姗€鏌嶈閸撶喎顫忕紒妯诲闁惧繐绠嶉埀顒€锕弻娑㈠箻鐎靛摜鐤勯梺杞扮椤戝懘鍩為幋锔藉€烽柛娆忣槸濞咃繝姊虹粙鍖℃敾缂佽鍊块敐鐐剁疀閹句焦妞介、鏃堝川椤撴繄鏁鹃梻鍌欑閹碱偊藝閹殿喒鍋撶粭娑樻搐绾捐銇勯弽顐沪闁抽攱鍨块弻娑樷槈濮楀牊鏁鹃梺鎶芥敱閸旀瑩寮婚敐澶嬪亜闁告瑥顦伴悵鏂款渻閵堝棙绌跨紒鎻掑⒔閹广垹鈹戦崱鈺傚兊濡炪倖鍨熼弬渚€寮查悩璇茶摕鐎广儱妫欐慨婊堟煙濞堝灝娅樻俊宸櫍閹鎲撮崟顒€纰嶅┑鈽嗗亝缁诲倿锝炶箛鎾佹椽顢旈崪浣诡棃婵犵數鍋為崹鍏肩椤掑嫬绀夐柟闂寸劍閳锋垹绱掔€n亜鐨¢柡鈧懡銈囩<閻犲洩灏欐晶鏇㈡煟閿濆洤鍘存鐐差儏椤潡顢旈崨顕呮閻庤娲忛崝鎴︺€佸▎鎴炲枂闁告洦鍋掓导鏍⒒閸屾艾鈧悂宕愰幖浣哥9闁归棿鐒﹂崑瀣攽閻樻彃顏柣顓熺懇閺岀喖鎮滃鍡橆€夋繝銏f硾鑹岄柡瀣叄閺岀喓鈧數顭堝暩闂佹寧绋掔划鎾愁潖閻戞闄勯柛娑橈攻閻濆磭绱撴担钘夌毢缂侇噮鍨崇划鈺呮偄閼茶櫣鍠庢晥闁搞儻濡囬惄搴ㄦ⒒娴e憡鎯堟繛鏉戝€圭粋宥夋倷閻㈢數鐓嬪銈嗘⒒閻℃柨鈻撴禒瀣厽闁归偊鍨辫ぐ褔鏌ら悧鍫濐嚋闁靛洤瀚版慨鈧柨娑樺閸n噣姊洪崫銉バ㈤柨鏇樺劚椤洩绠涘☉妯溾晝鎲歌箛姘e悁闂傚倸鍊搁崐鎼佸磹閹间礁纾归柣鎴eГ閸ゅ嫰鏌涢幘鑼槮闁搞劍绻冮妵鍕冀椤愵澀娌梺绋款儜缁绘繈寮婚弴锛勭杸閻庯綆浜栭崑鎾诲即閻樺樊妫滄繝鐢靛У绾板秹鎮″▎鎾寸厵妞ゆ牕妫楅懟顖氣枔閸撲胶纾藉ù锝呮惈閳诲牏绱掗悩宕囧⒌鐎殿喖顭烽弫鎰緞婵犲嫷鍟嬮梻浣告啞閸旀牞銇愰崘銊愭帡骞囬悧鍫氭嫽婵犵數濮存鍛婃櫠婵犳碍鐓曢柟鐐綑閸濈儤顨ラ悙鑼ⅵ濠碘剝鎮傞弫鍌炲礈瑜忓Σ鍥⒒娴e憡鍟炲〒姘殜瀹曟娊顢欓悾宀婃祫闂佸啿鎼崯鎵閽樺褰掓晲閸曨厾鐓撻梺鍛婄箖濡炰粙骞冩禒瀣垫晬婵炴垶蓱鐠囩偤姊洪幐搴g畼闁稿鐩垾锕傚Ω閳轰線鍞跺┑鐘绘涧濡粓鍩€椤掆偓閻忔繈鍩為幋锔藉€烽柛娆忣樈濡偟绱撴担铏瑰笡闁告梹鐗犻幃楦跨疀閹绢垱鏂€闂佺粯锚閻忔岸寮抽埡浣叉斀妞ゆ梹鍎抽崢瀵糕偓娈垮櫘閸嬪﹪鐛弽銊﹀闁告縿鍎荤槐杈ㄧ節閻㈤潧浠﹂柛顭戝灦瀹曞綊宕烽鐘辩瑝闂佺粯顭堝畷鐢稿矗閹剧粯鐓曢柕澶涚到婵¤棄鈹戦姘倯缂佺粯绋戦蹇涱敊閼姐倕鍤梻浣侯焾椤戝懐鈧凹鍠氬Σ鎰板箳閹宠櫕妫冨畷鐔煎煘閹傚闂侀€炲苯澧撮柡灞剧〒閳ь剨缍嗛崑鍛焊娴煎瓨鐓欑€瑰嫮澧楅崳浠嬫煕閺嶃劎澧电€殿喗鎸抽幃銏㈡偘閳ュ厖澹曟繝鐢靛У绾板秹鍩涢幋锔藉仭婵炲棗绻愰鈺呮煕閺傝鈧鎯€椤忓棛纾奸柕蹇曞Т缁秹鏌﹀Ο鑽ょ疄闁哄备鍓濆鍕偓锝夋涧閸斿苯鈹戦悙瀛樺碍妞ゎ厾鍏樺濠氬即閵忕娀鍞跺┑鐘绘涧濞村倸螞閵堝棛绡€闁冲皝鍋撻悘鐐舵椤偆绱撴担浠嬪摵閻㈩垳鍋ら崺鈧い鎺戯功缁夐潧霉濠婂懎浠﹂柡鍛埣閺佸倻绮电€n偒鍟嶉梻浣虹帛閸旀浜稿▎鎴犱笉鐎规洖娲ㄧ壕濂稿级閸稑濡肩紒妤佸浮閹藉爼鏁愭径瀣幘濠电偞娼欓鍡椻枍閹剧粯鐓曢柣鏃傚厴閸欏嫭鎱ㄦ繝鍐┿仢鐎规洦鍋婂畷鐔煎垂椤愬稄绠撳铏圭磼濮楀棙鐣跺┑鈽嗗亝閻熲晛顕i弻銉﹀殝闁汇垺顔栧ù鍕煟鎼搭垳绉靛ù婊呭仱钘濇い鎰剁悼缁犻箖鎮楅悽娈跨劸閻㈩垰鐖奸弻锝嗗箠闁告梹鍨块獮鍐灳閺傘儲鐎婚梺瑙勫劤椤曨參宕㈡ィ鍐┾拺閻犲洠鈧啿绠洪柣銏╁灡鐢€崇暦濠靛围濠㈣泛顑囬崢钘夘渻閵堝棙灏甸柛鐘叉捣缁叀顦归柡灞界Х椤т線鏌涢幘鏉戝摵妞ゃ垺鐟╁浠嬵敇閻愮數宕舵繝寰锋澘鈧洟骞婃惔锝囦笉闁哄稁鍘介悡鏇㈡倶閻愰潧浜鹃柣銊﹀灴閺岋繝宕遍銏☆€嶉梺閫涚┒閸斿矂鈥旈崘顏呭珰闂婎偒鍘奸ˉ姘舵⒒閸屾瑨鍏岀痪顓炵埣瀵彃鈹戠€n亞锛涢梺缁樺姇濡﹪宕靛Δ鍛厱闁哄洢鍔岄悘鐘裁归懖鈺佲枅闁哄本娲樼粩鐔碱敍濮橆剦浠惧┑鐐叉噺鐢帡鍩為幋锔藉亹婵炲牊瀵у▓鎵磽娴d粙鍝烘繛鑼枎閻g兘骞嬮敃鈧粻锝夋煥閺囨浜剧紒鐐劤缂嶅﹪寮婚垾鎰佸悑閹肩补鈧磭顔愮紓鍌欒閸嬫挸顭块懜闈涘闁绘挻鐟╁鍫曞醇濠靛棌鎸冮梺浼欑秮娴滃爼寮婚敓鐘茬闁宠桨绀佹慨锕傛⒑閸濆嫭婀伴柣鈺婂灠椤曪綁骞橀鍢夆晠鏌曟径鍫濈仼濞存粓绠栭弻锝呂熼懖鈺佺闂佺顑呯€氫即寮婚敐澶婄闁惧浚鍋呭畷鎶芥⒑閸涘﹥顥栫紒鐘冲灴閳ユ棃宕橀鍢壯囨煕閳╁喚娈橀柣鐔村姂閺岋絾鎯旈姀鐘叉瘓闂佸憡鐟ラ崯顐︽偩閻戣棄绠涢柣妤€鐗嗘禒娲⒑閸涘﹦鈽夐柨鏇樺€栫粋鎺楊敇閻愨晜鏂€闂佺粯鍔曞鍫曀夊鍛<缂備焦锚婵秵銇勯姀鈩冾棃妞ゃ垺妫冨畷鍗炩枎閹搭垳搴婇梻鍌欑窔閳ь剛鍋涢懟顖涙櫠閹绢喗鐓曢柍瑙勫劤娴滅偓淇婇悙顏勨偓鏍暜閹烘纾归柤濮愬€曢ˉ姘归悩宸剱闁绘挻娲熼幃姗€鎮欓棃娑楀闂佹眹鍔嶉崹褰掑焵椤掍胶鈯曠紒璇茬墕椤繐煤椤忓嫮顔囬柟鍏肩暘閸ㄥ鏁嶅鈧铏圭矙閸栤剝鏁剧紓浣筋嚙閻楁捇鎮伴鈧畷姗€顢欓挊澶嗗亾闁垮浜滈柟鐑樺焾濡插綊寮崼銉︹拺缁绢厼鎳庨ˉ宥夋煙濞茶绨界€垫澘锕畷绋课旀担闀愮暗闂備胶鎳撴晶鐣屽垝椤栫偞鍋傞柣鏂垮悑閻撶喐淇婇姘儓缂佺嫏鍛亾閻熺増鍟炵紒璇茬墦瀵鈽夊锝呬壕闁挎繂楠告禍婵嬫倶韫囷絽寮柟钘夌埣閹瑩鎮滃Ο鐓庡箞闂備線鈧稑宓嗘繛浣冲洤鍑犳繛鎴欏灪閻撴盯鏌涢弴妤佹珔闁告棑绠撻弻锛勪沪閻e睗銉︺亜瑜岀欢姘跺蓟濞戙垹绠婚柡澶嬪灥閹藉灚绻濈喊澶岀?闁轰浇顕ч悾鐑芥偄绾拌鲸鏅┑顔斤耿绾悂宕ú顏呪拻濞达絿鍎ら崵鈧梺瀹︽澘濡跨紓鍌涙尰閵堬綁宕橀妸褝绱遍梻浣筋潐閸庤櫕鏅舵惔锝咁棜闁稿繘妫跨换鍡樸亜閺嶃劍鐨戞慨锝囧仱閺岋紕鈧綆鍋嗘晶鐢告煙椤旂瓔娈滈柣娑卞櫍瀹曞綊顢欓悡搴經濠碉紕鍋戦崐褏绱撳璺虹闁规儼妫勭粻鏍煃閵夛附鐏辨俊鎻掔墛閹便劌顫滈崼銏犲煂婵炲瓨绮庨崑鎾汇€冮妷鈺傚€烽柤纰卞厸閾忓酣姊洪崨濠冣拹鐎光偓閹间礁钃熸繛鎴欏灪閸嬪棗霉閿濆娅滅紒銊ュ悑缁绘盯鏁愰崨顔芥倷闂佹寧娲╃粻鎾荤嵁閹达箑绀嬫い鏍嚤閳哄啯鍠愰煫鍥ㄧ⊕閺咁剚绻濇繝鍌滃闁抽攱鍨圭槐鎾存媴閻ч晲绶甸梺缁樺笒婢т粙鍩€椤掑喚娼愭繛鍙夌矒瀵偅绻濆顒傜暫闂佽鍨奸悘鎰洪宥嗘櫆闂佸憡渚楅崹浼寸嵁閹扮増鈷戦悹鍥皺缁犳娊鏌涚€n偆鈯曢柡鍛埣閹稿﹥绔熷┑鍥ㄣ仢妤犵偞锕㈤、娆撴偩鐏炶棄绠為梻鍌欑閻ゅ洤顩奸妸褏鐭嗗〒姘e亾妞ゃ垺妫冮、姗€鎮╅顫闁荤喐鐟ョ€氼厾绮堥崘鈹夸簻闁靛鍎婚煬顒傗偓瑙勬礃濡炰粙寮幘缁樺亹闁肩⒈鍓ㄧ槐鍙夌節濞堝灝鏋熼柨姘辨喐閺夋妯€妤犵偛鍟撮弫鎰板川椤忓懏鏉搁梻浣虹帛閸旀浜稿▎鎾崇闁绘鏁哥壕鍏笺亜閺冨洤浜归弫鍫澪旈悩闈涗粶闁哥喐娼欓悾鐑藉箳濡や礁鈧攱銇勮箛搴n槮濞存粍鍎抽湁闁挎繂鎳庨ˉ蹇旂箾缁楀搫濮傞柡灞界Х椤т線鏌涢幘璺烘灈闁绘侗鍣e畷姗€顢欓懖鈺佸箰闂備礁鎲℃笟妤呭窗閺嶃劎顩烽柧蹇撴贡绾惧ジ鏌i幇闈涘缂佽泛寮堕妵鍕晝娓氣偓閸濇椽鏌熼娑欌拹缂佺粯绻堝畷鍫曞Ω閵忊€愁伜闂傚倷鑳堕…鍫ュ嫉椤掑嫭鍋¢柕濞炬櫅缁€鍌溾偓鍏夊亾闁逞屽墰濡叉劙骞掑Δ濠冩櫔闂佸憡渚楅崢鐐閹间焦鈷戦悹鍥b偓铏亾闂佺绻戦敃銏狀嚕椤愶箑绀冩い鏃囧亹閿涙粌鈹戦悙鏉戠仸閻鏌i姀鐙€鐓兼慨濠勭帛缁楃喖鍩€椤掆偓椤洩顦归挊婵囥亜閹惧崬鐏╃痪鎹愭硶閳ь剙绠嶉崕閬嶅箖閸啔娲敂瀹ュ棙娅嗛梻浣告啞娓氭宕板Δ鍛仧闁哄稁鍘介埛鎺懨归敐鍕劅闁绘帡绠栭弻锟犲醇椤愩垹顫紓渚囧枟閻熲晠鐛€n喗鍊锋繛鍫熷闁裤倖绻濆閿嬫緲閳ь剚鍔欏畷鎴﹀箻缂佹鍘撻柣鐔哥懃鐎氼剟鎮橀幘顔界厵妞ゆ梻鏅幊鍥┾偓瑙勬穿缁叉儳顕ラ崟顐嬬喐瀵煎▎鎴狅紲闂傚倸鍊搁崐椋庣矆娴i潻鑰块梺顒€绉埀顒婄畵瀹曞ジ濡烽埗鈺佷壕闁挎洍鍋撻柣锝忕節楠炲秹顢欓懞銉晭闂傚倷娴囬~澶嬬珶閸℃ɑ娅犳俊銈呮噹绾惧鏌曟繛鐐珕闁绘挻娲樼换娑㈠箣閻戝洤鍙曢梺鍛婃⒒閸犳牠寮诲☉妯滅喖宕烽鐘靛幆婵犳鍠栭敃銉ヮ渻閽樺)娑㈠礃閵娿垺顫嶅┑顔筋焾娴滎剟寮抽悧鍫㈢瘈缁剧増锚婢ц尙鎲搁弶鍨殻妤犵偛锕よ灒闁惧繗顫夊▓鎯ь渻閵堝棛澧紒璇插閹潡鍩€椤掆偓閳规垿鎮欓弶鎴犱桓闂佽崵鍟欓崶褍鍋嶆繛瀵稿Т椤戝棝鍩涢幋锔界厱闁挎棁顕ч獮鏍煕閺傛鍎旈柡灞剧洴婵℃瓕顦抽柡鍡╁墴閺屾盯鍩¢崒婊勫垱閻庢鍣崜娆掔亱闂佹眹鍨归悘姘跺吹閳ь剙顪冮妶搴″箲闁告梹鍨甸悾鐑芥偄绾拌鲸鏅i梺缁樻⒒椤牓寮查崫銉х=闁稿本鑹鹃埀顒傚厴閹虫鎳滈崹顐㈠伎闂佹眹鍨归幉锟犲磿鎼搭潿浜滈柡宥庡亜娴犙呪偓瑙勬尫閻掞箓骞堥妸銉富閻犲洩寮撴竟鏇熶繆閻愵亜鈧垿宕归搹鍦煓闁硅揪绠戦悡鈥愁熆鐠哄彿鍫ュ几鎼淬劍鐓欓梺顓ㄧ畱楠炴﹢鎮介姘棦婵﹤顭峰畷鎺戭潩椤戣棄浜鹃柟闂寸绾惧綊鏌i幋锝呅撻柛銈呭閺屾盯骞橀懠顒夋М闂佹悶鍔嶇换鍐Φ閸曨垰鍐€妞ゆ劦婢€缁爼姊洪幖鐐插闁稿﹤鐏濋~蹇旂節濮橆剟鍞堕梺缁樻⒒閸庣敻宕戦幘缁樺癄濠㈣绻冨浠嬨€侀弮鍫濈閹煎瓨蓱濞呭洭鏌熼崣澶屾憙缂佺姵绋戦埥澶娾枎韫囨挸顥楅梻鍌欒兌閹虫挻鏅堕悾灞藉灊妞ゆ牜鍋為崑鍌炴煟閺傚灝鎮戦柣鎾崇箻閻擃偊宕堕妸锔绢槬闁哄稄绻濆娲传閵夈儲鐏侀梺绋款儍閸婃繂顕f繝姘櫜濠㈣泛锕﹂鎺楁煟鎼淬垻鈯曟い顓炴喘钘濆ù鐓庣摠閳锋垿鏌涘┑鍡楊伂妞ゎ偓绠撻弻娑㈠棘鐠恒劎鍔梺绯曟櫇閸嬨倝鐛€n喗鏅濋柍褜鍓熼悰顕€濮€閿涘嫮顔曢梺绯曞墲閿氶柣鎺楃畺閺屾盯鎮欓懜娈夸哗缂備浇椴搁幑鍥х暦閹烘垟鏋庨柟鎼幗琚﹀┑锛勫亼閸娧呯磽濮樺崬鍨濇繛鍡楃箳閺嗭箓鏌℃径瀣靛劌婵炲皷鏅犻幃瑙勩偊閹稿寒浠╅梺鍛婃缁犳垿鈥旈崘顔嘉ч柛鈩冾殘閻熸劗绱撴担绛嬪晣缂佺粯绻傞悾鐑筋敍濠靛牏鏉稿┑鐐村灦閻熝囧储闁秵鈷戠紓浣光棨椤忓棗顥氭い鎾跺枑濞呯娀鏌i姀鐘冲暈闁绘挸鍟撮弻鏇熷緞濡櫣浠梺浼欑悼閺佸寮婚悢纰辨晩闁伙絽鐬奸悡澶愭⒑閸︻収鐒鹃柨鏇樺劚椤曘儵宕熼娑樹壕闁挎繂楠搁崢鎾煕鐎n偅宕屾い銏☆殜瀹曠喖顢栭懞銉ヮ伖闂傚倷绶氬鑽も偓闈涚焸瀹曘垺绺介幖鐐╁亾閸岀偛绀傞柤娴嬫櫇閻﹀牓姊洪棃娑氱畾婵℃彃瀚伴幊鎾诲锤濡や胶鍘藉┑鐐村灥瀹曨剙鈻嶅鍛斀妞ゆ梻鎳撴禍楣冩⒒娴e搫浠洪柛搴☆嚟娴滅鈻庨幋鐘辩瑝濠殿喗锕╅崜锕€銆掓繝姘厪闁割偅绻冮ˉ鐘差熆瑜滈崜娑㈡儉椤忓牆绾ч悹鎭掑壉瑜庨〃銉╂倷閸欏妫﹂悗瑙勬礈閸樠囧煘閹达箑绀冮柍鍝勫€瑰鎴︽⒒閸屾瑧鍔嶉柡瀣偢瀵彃鈽夐姀鐘垫焾濡炪倖鍔х粻鎴︽偂濠靛鐓涢柛銉㈡櫅閺嬫垿鏌涘▎蹇曠闁宠鍨块幃鈺呭箵閹烘繀绱戦梺姹囧焺閸ㄨ京绮欓幘鑸殿潟闁圭儤鍤﹂弮鍫濈闁靛濡囨禍顏堟⒒娴h櫣銆婇柡鍌欑窔瀹曟垿骞橀幇浣瑰瘜闂侀潧鐗嗗Λ妤呭锤婵犲洦鐓曢悗锝庡亝鐏忎即鏌曢崶褍顏い銏★耿閹瑧鈧數纭堕弫宥嗕繆閻愵亜鈧呯不閹寸姷绀婂┑鐘叉搐閽冪喖鏌i弮鍌楁嫛闁轰礁锕弻鏇熺箾閸喖濮曢梺鐟板悑閸旀牠銆冮妷鈺傚€锋い蹇撳娴犲墽绱撴担铏瑰笡闁烩晩鍨伴悾鐑藉础閻愬秵妫冨畷鐔碱敃椤愶紕纾惧┑鐘垫暩閸嬫盯鎮洪妸褍鍨濋幖娣妼绾惧鏌熼幑鎰厫鐎规洖寮剁换娑㈠箣濞嗗繒浠肩紓浣哄缂嶄線寮婚敐澶婄疀妞ゆ牗姘ㄥВ銏ゆ⒑閼姐倕鏋戠憸鏉垮暣閸╃偤骞嬮敂钘夆偓鐑芥煕濞嗗浚妲告繛鍜冪到閳规垿鎮欓懠顒佸嬀闂佸憡鏌ㄦ绋垮祫闂佸湱澧楀妯肩不閹惰姤鐓欓柟顖嗗苯娈剁紓浣割槸閻栫厧顫忛搹鍏夊亾閸︻厼校闁靛棗鍟穱濠囨倷閺夋垹鐟ㄩ柛妤呬憾閺岀喖骞嶉纰辨毉闂佺锕﹂弫濠氬箖瀹勬壋鏋庨煫鍥ㄦ惄娴犲墽绱撴担鎻掍壕闂佸壊鍋侀崕鏌ユ偂閺囩喍绻嗘い鏍ㄧ矊瀛濆┑鐐茬湴閸婃繈骞冮垾鎰佹建闁逞屽墴瀵鎮㈤崨濠勭Ф闂佸憡鎸嗛崨顔筋啅缂傚倸鍊风拋鏌ュ磻閹剧粯鐓曢柟浼存涧閺嬬喖鏌i幘鍐叉殻闁哄本绋戦埞鎴﹀幢濡ゅ﹣鎮i梻渚€鈧偛鑻晶浼存煙閾忣偅宕岄柍銉畵瀹曠螖閳ь剛绮婚敐澶嬬叆闁哄啫娉﹂幒妤€绠┑鐘崇閳锋垹绱掔€n偄顕滄繝鈧导瀛樼厽闁绘梹娼欐慨鍌溾偓瑙勬礃椤ㄥ懘鎮惧┑瀣劦妞ゆ帒鍊归~鏇㈡煙閻戞﹩娈㈤柡浣割儔閺屾稑鈽夐崡鐐茬婵炲濮甸幃鍌炲箖濡ゅ啯鍠嗛柛鏇ㄥ墰椤︺劎绱撴担绛嬪殭闁稿﹤娼″畷娲閳╁啫鍔呴梺闈涱焾閸庢娊顢欓幒妤佲拺闂侇偆鍋涢懟顖涙櫠閹绢喗鐓欐い鏃傛櫕閻帡鏌熺粙鍖℃敾鐎垫澘瀚悾婵堚偓锝庡墮缁ㄣ儵姊婚崒姘偓鐑芥嚄閸撲礁鍨濇い鏍仜缁€澶愭煛瀹ュ骸鍘靛ù婊冪秺閺屾盯骞囬棃娑欑亪缂備胶濮靛畝鎼佸蓟閿濆绠涙い鏃傚帶婵℃椽姊虹紒妯诲暗闁哥姵鐗犻悰顕€寮介鐐殿啇濡炪倖鎸鹃崑鐔哥椤栨粎纾藉ù锝呭濡叉椽鏌℃担鍓茬吋鐎殿喛顕ч埥澶愬閻樻鍟嬮梺璇查閻忔岸骞冮崼鏇炵劦妞ゆ帊绀佺粭鎺撱亜椤撯剝纭堕柟鍙夋尦瀹曠喖顢楅崒銈喰炵紓鍌氬€峰ù鍥ь浖閵娧冨灊婵炲棗绻掗弳锕傛煏婵犲繐顩紒鈾€鍋撻梻浣告啞濞诧箓宕戦崟顓犱笉闁告繂瀚ч弨浠嬫煟濡椿鍟忛柡鍡╁灡娣囧﹪骞撻幒鎾虫畻閻庤娲濋~澶婎焽韫囨稑鐓橀柟顖嗗倸顥氱紓鍌欑劍椤ㄥ棛绮欓幋婢濇椽鏁冮崒姘憋紱闂佺粯姊归幃鑸电濠婂牏鍙撻柛銉e妽鐏忛潧顭胯閻╊垶寮诲☉娆戠瘈闁稿本绮岄悡鐔兼⒑缂佹ɑ鎯勯柛瀣工閻g兘鎳滃▓鎸幮ч柟鑲╄ˉ閳ь剙纾崢鎺楁⒑鐠囨彃顒㈡い鏃€鐗犲畷鎶筋敋閳ь剙鐣烽幎鑺ユ櫜濠㈣泛锕ㄩ幗鏇㈡⒑閻愯棄鍔氱痪缁㈠弮瀵娊宕卞☉娆忊偓鐢告煥濠靛棝顎楀褎澹嗛幃顕€鏁冮崒娑掓嫽婵炶揪缍€婵倝濡撮崘顔界厽闁硅櫣鍋熼悾鐢碘偓瑙勬礃缁诲倿鍩㈡惔銈囩杸闁哄洨鍠愰鏇㈡⒒娓氣偓濞佳嗗闂佸搫鎳夐弲鐘差嚕椤愶箑鐐婃い鎺嶈兌閸樹粙姊洪崫鍕殜闁稿鎸搁…璺ㄦ喆閸曨剛顦伴悗娈垮枟瑜板啴鍩ユ径鎰厬闁宠鍎虫禍楣冩煛閸愩劎澧曠紒鈧崘鈹夸簻闁哄倹瀵ч~宥囨喐閺冨牏宓侀柡宥庡亜閸ㄦ繈鏌涜箛鎿冩Ц濞存粌澧介埀顒冾潐濞叉牕霉閸岀偛鑸圭憸鐗堝笚閳锋帡鏌涚仦鍓ф噮妞わ讣绠撻弻鐔访圭€Q冧壕闁归鐒︾紞搴ㄦ偡濠婂懎顣奸悽顖涘浮瀹曞綊宕掗悙瀵稿幗闂侀潧绻掓慨鐢稿疮閻愮儤鐓曢悗锛卞嫭鐝氬┑顔硷攻濡炶棄鐣疯ぐ鎺濇晪闁告侗鍘兼竟瀣⒒閸屾艾鈧摜鈧凹鍓涢埀顒佺煯閸楀啿顕g拠娴嬫婵☆垶鏀遍~宥呪攽椤旂瓔娈旈柣妤€妫欑€靛ジ骞囬鐘殿啎闁诲孩绋掗…鍥儗鐎n剛纾兼い鏃囧Г鐏忣厽銇勯銏㈢閻撱倖銇勮箛鎾村櫣闁逞屽墴閺€閬嶅Φ閸曨垰绠抽柟瀛樼箖濞堫厼顪冮妶鍐ㄥ姕缂佽鐗嗛~蹇涙惞閸︻厾鐓撻梺鍛婄墤閳ь剙鍘栫槐锝嗕繆閻愵亜鈧倝宕㈡ィ鍐ㄧ婵せ鍋撻柣娑卞櫍瀹曞崬鈽夊Ο纰辨Ч婵$偑鍊栫敮濠勭矆娓氣偓瀹曟繈宕ㄧ€涙ǚ鎷洪梻鍌氱墛缁嬫挾绮婚悙鐑樼厱闁靛鍎洪悡濂告煙椤栨瑧绐旂€规洖銈告慨鈧柕蹇f緛缁辨煡姊绘担铏瑰笡闁告棑绠撳畷婊冾潩鏉堫煈鍋ㄩ梺鍛婄懃椤︻厽绂嶅鍫熺叆闁哄洦纰嶉ˇ鐑芥煕濮樼厧浜滄い顓℃硶閹叉挳宕熼鍌ゆЧ闁诲氦顫夊ú婊堚€﹂崼锝囦簷濠电偠鎻徊浠嬪箹椤愶妇宓侀柛顐犲劜閳锋垿鎮归崶銊ョ祷闁搞倛浜槐鎾愁吋閸涱噮妫﹂悗瑙勬礃閸ㄥ灝鐣烽崡鐑嗘富闁哄洠鍓濋鐘绘煃瑜滈崜姘辩矙閹烘洖缍樺┑鐐茬摠缁秶鍒掗幘璇茶摕闁哄浄绱曢悿鈧梺闈涳紡閸滃啰鍚规繝鐢靛Л閹峰啴宕ㄩ鑺ョ槑闂備線鈧偛鑻晶鍙夈亜椤愩埄妲搁悡銈夌叓閸ャ劎鈽夌紒鈧径鎰厵閺夊牊宕樼粈瀣煃瑜滈崗娑氱矆娓氣偓閸┿儲寰勬繛銏㈠枎椤劑宕熼澶嬵棃闂備胶纭堕弬渚€宕戦幘鎰佹富闁靛牆妫楃粭鍌炴煠閸愯尙鍩i柕鍡楁嚇瀵濡烽敂鎯у箺闂備線鈧稑宓嗘繛浣冲嫭娅犻柟娈垮枤绾惧ジ鏌eΟ鍨惞闁伙絾妞介弻鈥崇暆閳ь剟宕伴幘璇茬劦妞ゆ帒鍊归弳鈺傘亜椤撶偟澧涚紒鍌涘笒椤劑宕ㄩ婊愮床婵犲痉鏉库偓鎾绘嚄閸洏鈧倿鎳犻鍌滐紲缂傚倷鐒﹂…鍥虹€电硶鍋撶憴鍕8闁告梹鍨块妴浣割潨閳ь剟骞冮姀銈嗙叆閻庯綆鍓氬В鍫ユ⒒閸屾艾鈧绮堟笟鈧獮鏍敃閿旇棄娈e銈嗙墬缁酣鎯岄幘缁樼厱闁规崘灏欓崝宥嗐亜椤愶絾绀嬮柡宀€鍠栭幃婊兾熼悜姗嗗晭闂備胶绮濠氬磿閵堝洠鍋撳顓炲摵闁哄被鍊楅崰濠囧础閻愭祴鎸勭紓鍌欑劍閸炶崵绮婚幋锕€鐓橀柟瀵稿仜缁犵娀姊虹粙鍖℃敾妞ゃ劌妫濋獮鍫ュΩ閳哄倸鈧鏌﹀Ο渚Ш闁挎稒绋戦埞鎴︽倷閺夋垹浠稿銈庡幖閸婃悂鍩ユ径濠庢建闁糕剝鐟ュ鎶芥⒒娴h櫣銆婇柡鍛仜閳绘柨鈽夊Ο蹇旀そ椤㈡﹢锝為钘変壕濞达絽澹婂鈺呮偣妤︽寧顏犻柛鏃撶畱椤啴濡堕崱妤冪懆闁诲孩鍑归崜鐔煎箯閹达附鍋勯柛蹇氬亹閸欏棝姊虹紒妯荤叆闁圭⒈鍋勯悺顓㈡⒒娴h櫣甯涢悽顖涘浮閹ê顫濈捄浣曪箓鏌涢弴銊ョ仩缂佺姴纾埀顒€绠嶉崕閬嶆偋閸℃稑鍌ㄩ柍銉﹀墯濞撳鏌曢崼婵嗏偓鐟扳枍閸ヮ剚鐓曢煫鍥ㄦ閼版寧顨ラ悙鎻掓殭閾绘牠鏌涘☉鍗炴灍婵炲懏绮撻弻鐔兼嚃閳哄媻澶愭煃瑜滈崜婵堜焊濞嗘挸鏋侀柡宥庡幗閳锋帒霉閿濆懏鍟為柛鐔哄仦閵囧嫰顢橀悙闈涱暫闁捐崵鍋ら弻娑㈠即閵娿儳浠╅梺缁樻尰閿曘垽寮婚悢鍛婄秶闁告挆鍛闂備胶绮幖顐ゆ崲濠靛钃熸繛鎴欏灩閻掓椽鏌涢幇顔间壕闁伙絽鍚嬬换娑氣偓鐢殿焾椤庡矂鏌涘Ο鎭掑仮闁炽儲妫冨畷姗€顢欓崲澹洦鐓曢柍鈺佸枤濞堟ê霉閻樿櫕鍊愭慨濠冩そ閹筹繝濡堕崨顔界槪闂備礁鎼幊蹇涙儎椤栫偛绠栧Δ锝呭暞閸婂鏌ら幁鎺戝姎濞寸姾娅g槐鎺楀礈瑜嶉。濂告煥濮橆優鐟邦煥閸垻鏆梺鍝勮閸斿矂鍩為幋锕€骞㈡繛鎴炲閸嬫挸螖閸涱喚鍘卞┑鈽嗗灣缁垳浜搁敃鍌涚厸閻忕偛澧介妴鎺楁煃瑜滈崜銊х礊閸℃稑纾婚柛娑卞灟閻掑﹪鏌i姀鐘冲暈闁绘挻鐟╅弻娑樷枎韫囷絾效闁诲繐楠忔俊鍥焵椤掑喚娼愭繛鍙夌矒瀹曚即寮介婧惧亾娴h倽鏃堝川椤撶姴濮︽俊鐐€栫敮濠囨嚄閸洏鈧懘鎮滈懞銉у帗闂佸憡绻傜€氼參宕冲ú顏呯厓闂佸灝顑呴悘鈺冪磼鏉堛劌绗ч柍褜鍓ㄧ紞鍡涘磻閸曨垼鏁嬫繝濠傜墛閻撴瑩鏌h閹芥粎绮旈鈧弻锛勪沪缁嬪灝鈷夐梺鐟板槻閹虫劗鍒掗悽纰樺亾閿濆簼绨兼い鏂垮娣囧﹪鎮欓鍕ㄥ亾閺嶎灐娲煛閸愩劎绛忛梺鍛婃寙閸曨偄绨ユ繝鐢靛█濞佳兾涢鐑嗙劷闁冲搫鍊舵禍婊堟煙閹规劖纭鹃柡瀣灴閺岋絽鈹戦崶褉鏋欏┑顔硷功缁垶骞忛崨鏉戝窛濠电姴鍊瑰▓妯肩磽閸屾瑧顦︽い鎴濇瀹曞綊宕归鐐闂佽澹嗘晶妤呭磻閿熺姵鐓欓梺鍨儐閳锋劙鏌i埡濠傜仩闁伙絽鍢查~婊堝焵椤掑嫨鈧礁鈻庨幘宕囶槯闂佺绻愰妵娆忣潩閼哥鎷绘繛鎾村焹閸嬫捇鏌嶈閸撴盯宕戝☉銏″殣妞ゆ牗绋掑▍鐘炽亜閺嶎偄浠﹂柣鎾崇箻閺屾盯濡烽幋婵嗘灓濞寸厧鍟灃闁绘﹢娼ф禒锕傛偨椤栨せ鍋撳畷鍥ㄦ闂佸憡顨堥崕鎰€掓繝姘厵妞ゆ牕妫楅張顒勊夐敓鐘斥拻闁稿本鑹鹃埀顒傚厴閹偤鏁冮埀顒勬偩瀹勬嫈鐔兼惞鐟欏嫭顔曢梻浣圭湽閸ㄥ鈥﹂崼銏狀棜濠电姵纰嶉悡鐔兼煙闁箑澧板ù鐘崇〒閳ь剝顫夊ú鏍ь嚕閸撲焦宕叉繛鎴欏灩缁狅絾绻涢崱妤冪濞寸姾鍋愮槐鎾存媴閸濆嫷鈧挾绱撳鍕獢鐎殿喖顭烽弫鎰緞婵犲嫮鏉告俊鐐€栭悧妤冪矙閹捐违闁归偊鍓﹀〒濠氭煏閸繂鏆欓柛鏃€绮庣槐鎺旀嫚閼碱剙顣哄銈庡亜缁绘劗鍙呭銈呯箰鐎氼噣顢欓幇鐗堚拺缂備焦锚婵牏鎲搁弶鍨殻闁炽儲鐗楀鍕暆閳ь剛澹曢挊澹濆綊鏁愰崶鈺傛啒闂佹悶鍊栭悷鈺呭蓟濞戞瑧绡€闁稿本绋戞禒鎾倵鐟欏嫭绀冩俊鐐扮矙楠炲啫鈻庨幘鍏呯炊闂佸憡娲﹂崣搴ㄥ触閸涘瓨鈷掑ù锝囨嚀椤曟粍淇婇锛勵槮閾荤偤鏌涢弴銊ュ妞も晞灏欓幉鎼佹偋閸繄鐟查梺缁樻尵閸犳牠鐛弽顐㈠灊闁荤喐婢橀埛澶愭煟閻樺啿濮€闁逞屽墯閺嬪ジ寮ㄩ懞銉d簻闁哄啫娲よ闁诲繐楠忕粻鎾诲箰婵犲洦鍋勯柛婵勫劤閻﹀牓姊婚崒姘卞濞撴碍顨婂畷鏇㈠箛閻楀牏鍘介梺瑙勫劤閻°劎绮堢€n喗鐓涚€光偓鐎n剛袦濡ょ姷鍋涢鍛村煘閹达箑鐐婇柤鍛婎問濡囨⒒閸屾瑦绁版い鏇嗗嫷娈介煫鍥ㄧ⊕閳锋棃鏌涢弴銊ョ仩缂佺姷鍋ら弻鏇熺節韫囨搩娲紓浣叉閸嬫捇姊绘担鍛婂暈闁告柨绻樺顒勫磼濞戞凹娴勯梺闈涚箳婵牓寮崼鐔蜂汗闂傚倸鐗婄粙鎰柦椤忓牊鈷戦柛娑橈攻閳锋劙鏌eΔ鍐ㄢ枅闁绘侗鍣e畷鍗炩槈濡偐娼夐梻浣稿閸嬪懐鎹㈠鍜佺劷濠电姴娲﹂埛鎴︽煕閹邦剙绾ч柟顖氱墦閺屾稒绻濋崟顒佹瘓濡ょ姷鍋為崝娆忕暦閵娾晩鏁囨繛鎴炵懄閺夋悂姊绘担铏瑰笡閽冭鲸銇勯弮鈧悧鐘差嚕閹剁瓔鏁嶉柣鎰嚟閸橀亶姊虹憴鍕姢妞ゆ洦鍘剧划濠氭倷濞村鏂€闂佽法鍠撴慨闈涒槈瑜庨妵鍕敇濠婂啫顫囬悗瑙勬礈閸樠囧煘閹达箑閱囨い鎰跺強閵夆晜鈷掑ù锝囧劋閸も偓闂佸憡鑹鹃澶愬箖妤e喚鏁傞柛顐g箘椤︻噣鎮楅獮鍨姎妞わ富鍨跺畷銉╁捶椤撴稑浜炬鐐茬仢閸旀碍銇勯敂璇茬仯闁汇儺浜iˇ褰掓煛鐏炲墽娲存い銏℃礋閺佹劙宕堕敐鍡╂綌婵犵數濮撮惀澶愬Χ閸℃瑣鈧﹦绱撴担浠嬪摵閻㈩垽绻濆畷娲晝閸屾氨鍔﹀銈嗗笒鐎氼剛澹曟繝姘厵闁诡垎灞芥缂備讲妾ч崑鎾寸節閻㈤潧浠滈柣妤€妫濋幃妯衡攽鐎n亜鍤戦梺缁樻煥閸氬鎮¢妷鈺傜厸闁搞儺鐓堝▓鏇熺箾閸涱叏鍔熼柍褜鍓濋~澶娒鸿箛娑樺瀭濞寸姴顑囧畵渚€鏌″鍐ㄥ濠殿垱鎸抽弻娑樷攽閸曨偄濮堕梺鍝ュ仜閻忔氨鎹㈠┑瀣仺闂傚牊绋愮划璺衡攽閳藉棗鐏犻柨鏇樺劤缁顓奸崨顏呮杸闁诲函缍嗘禍鐐哄储闁秵鈷戠痪顓炴噺瑜把囨⒒閸曨偄顏柟顕嗙節瀵挳鎮㈤搹璇″晭闂備胶鎳撻顓㈠磿閹达箑绀傛い鎺戝閻撴洟鏌¢崘銊モ偓鎼佸几閺冨倻纾奸弶鍫涘妼濞搭噣鏌熼瑙勬珚闁圭厧缍婇、鏇㈠椤喚澶勯梻鍌氬€峰ù鍥敋閺嶎厼绐楁俊銈呮噷閳ь剙鍟村畷銊︽綇閸撗呪棨婵犵數濞€濞佳囶敄閸℃稑纾婚柛宀€鍋涚粻鍦磼椤旀娼愭い搴℃閺岀喐绺芥径濠佸枈濠殿喖锕︾划顖炲箯閸涘瓨鎯炴鐐茬氨閸嬫挻绻濋崶銊у幐闂佺鏈悷褏绮i弮鍌楀亾鐟欏嫭绀冮柛銊ユ健閻涱喖顫滈埀顒勭嵁閸ャ劍濯撮柣鐔稿濡诧綁姊婚崒娆戠獢婵炰匠鍥ㄥ亱闁糕剝銇傚☉妯滄棃宕橀鍡欐殽闂備胶顭堥惉濂稿磻閻愮儤鍋傞柣鏂垮悑閻撴瑩鏌ц箛鏇熷殌濞寸姍鍥ㄧ厽闁挎繂娲﹂弳鈺呮煃瑜滈崜婵嬶綖婢跺⊕鍝勵潨閳ь剙鐣峰┑鍡忔瀻闁规崘娉涚粊锕傛⒑閹肩偛鍔撮柛鎾村哺瀹曟垹鈧綆鍠楅悡鏇熴亜閹邦喖孝闁诲繆鏅滈〃銉╂倷閼碱儷锝吳庨崶褝韬柟顔界懇椤㈡棃宕熼妸銉ゅ闂佸搫璇炵仦鍓х▉濠电姷鏁告慨鐢靛枈瀹ュ纾婚柛灞剧◤娴滄粓鏌熼幏灞剧【闁伙附绮撻弻鈩冩媴缁嬪簱鍋撻崸妤€钃熸繛鎴欏焺閺佸啴鏌ㄥ┑鍡樺窛闁伙絽銈稿娲川婵炴碍鍨块獮鎰板礃瀹割喗缍庡┑鐐叉▕娴滄繈宕戦敓鐘斥拺妞ゆ挶鍔庨悾杈ㄧ箾閸絽鐓愮紒缁樼箓閳绘捇宕归鐣屽蒋闂備礁鎲¢悷銉╁疮椤愶附鍋╅柣鎴f缁狅綁鏌ㄩ弴妤€浜剧紓浣哄Ь瀹曠數妲愰幘瀛樺闁兼祴鍓濋崹鐢稿煝瀹ュ拋鐓ラ柛顐ゅ枔閸樼敻姊虹紒妯诲碍婵炲鍏橀獮妤呮偐閻㈢數锛滈柣鐘叉处瑜板啴顢旈鐘亾濞堝灝娅橀柛瀣工椤曪絾绂掔€e灚鏅i梺缁樻煥瀵墎鈧艾銈稿缁樻媴閸涘﹤鏆堢紓浣割儐閸ㄥ潡鍨鹃敃鍌ゆ晣闁靛繆鈧櫕鐣梻浣稿閻撳牓宕弮鍫熷仭闂侇叏濡囬崣鍡涙⒑缁洖澧叉い顓炴喘婵℃挳骞囬澶嬪瘜闂侀潧鐗嗘鍛婄濠婂懐纾肩紓浣姑慨澶愭煕濞嗗繑鍣规い顏勫暣婵″爼宕ㄩ婊庡敹闂佽瀛╅崙瑙勭閻愬弬锝夊箛閺夊潡鍞堕梺鍝勬川閸熷潡骞忓ú顏呪拺闁告稑锕﹂埥澶愭煥閺囨ê鍔滅€垫澘瀚板畷鐔碱敍濞戞艾骞堥梺璇插嚱缂嶅棙绂嶅┑瀣棷鐟滅増甯楅悡鍐磽娴h偂鎴濈暦鐏炰勘浜滈柕蹇婃閼板灝鈹戦鐟颁壕闂備焦濞婇弫顕€宕戦幘缁樼厵闁汇値鍨遍鐘电磼鏉堛劍宕岀€规洘甯掗埢搴ㄥ箣濠靛棭鐎撮梻鍌欑劍鐎笛兠哄澶婄柧婵炴垯鍨归悡婵嬫煙閹规劦鍤欑紒顐㈢Ч閺屾盯顢曢妶鍛亖闂佸憡鐟ュΛ婵嗩潖濞差亜浼犻柛鏇ㄥ墮閸嬪秹姊洪崨濠冪叆妞ゆ垵顦靛濠氬炊椤掑鏅┑鐐村灱妞存悂顢欓弮鍫熲拺缂備焦锚婵牏鎲搁弶鍨殻鐎殿喗濞婇弫鎰緞鐎n剙骞愬┑鐐舵彧缂嶁偓妞ゎ偄顦悾宄扮暆閸曨剛鍘靛銈嗘椤鈻嶆繝鍕ㄥ亾鐟欏嫭绌跨紓宥勭閻g兘骞掗幊宕囧枛瀹曨偊宕熼崹顐ょУ闂傚倸鍊风粈渚€骞栭銈嗗仏妞ゆ劧绠戠粈澶愭煙鐎涙绠ラ柛銈嗘礃閵囧嫰骞掗幋婵愪患闂佹悶鍔岄崐褰掑Φ閸曨垰绫嶉柛銉ㄥ煐缂嶅牓鏌f惔锛勪粵闁绘顨嗙粚杈ㄧ節閸ャ劌鈧攱銇勮箛鎾愁仱闁稿鎹囧鍊燁檨婵炲吋鐗犻弻锝夋偄缁嬫寧鐝靛┑鐐叉▕娴滄繈宕戦崟顐熸斀闁稿本鍑瑰Σ鍦磽瀹ュ懘顎楅柍瑙勫灴閹瑩宕f径鍡樼亞濠电偛鐡ㄧ划宥囨崲閸繄鏆﹂柟杈鹃檮閺呮悂鏌eΟ缁樼伇闁瑰嘲鎼—鍐Χ閸℃ê钄奸梺鍛婃煥闁帮綁骞冮悙顒佺秶闁靛ě鍜佸晭闂備礁澹婇崑鍛崲閸曨垰鏄ラ柨婵嗘閸欏繐鈹戦悩鍙夊櫤妞ゅ繒濮风槐鎺楊敊閻e本鍣ч梺瀹狀嚙闁帮綁鐛崱姘兼Щ婵犮垻鎳撻澶婎潖缂佹ɑ濯撮柛娑橈攻閸犳劖绻濆▓鍨灓闁轰礁顭烽獮鍐樄闁诡喒鏅濈槐鎺懳熸潪鎵挼濠碉紕鍋戦崐鏍ь潖婵犳艾鐤炬い鎰╁€曟慨顒勬煃瑜滈崜鐔奉潖濞差亜绠归柣鎰絻婵⊙囨⒑閸涘﹤濮﹀ù婊呭仜閻g兘宕崟銊︽杸闂佹寧绋戠€氼剚绂嶆總鍛婄厱濠电姴鍟版晶鐢告煙椤斻劌鍚橀弮鍫濈闁靛鍎虫禍浼存⒑閻熸澘鎮戦柣锝庝邯瀹曟繂顓兼径濠勬煣濡炪倖甯婇懗鍓佸姬閳ь剚绻濋悽闈浶㈤柛濠勭帛閺呰泛鈽夐姀锛勫帗闂備礁鐏濋鍛存倶閳哄啰纾奸弶鍫涘妽鐏忎即鏌熷畡鐗堝殗鐎规洘顨嗗鍕偓锝呭缁€鍕攽閿涘嫬浜奸柛濠冩礈閹广垽骞囬鈺傜☉铻栭柛姘虫椤︻垶锝炲┑瀣垫晣婵犲ň鍋撶紒銊ヮ煼濮婅櫣鎲撮崟顐ゎ槰濠电偛顦伴惄顖氼嚕閹间礁绠i柣鎰暩椤旀洟姊洪崨濠佺繁闁搞劋鍗抽崺銏ゅ醇閳垛晛浜炬繛鍫濈仢閺嬫盯鏌i弽顐㈠付闁伙絿鍏橀幃鈩冩償椤旇棄鍏婃俊鐐€栭幐楣冨窗閹惧箍浜归柛銉㈡櫇绾捐棄霉閿濆懏鎯堝ù婊堢畺閺屾稒鎯旈姀鐘灆婵犵鈧啿顣崇紒顔界懃閳诲酣骞嗚椤撳潡姊绘担绋款棌闁稿鎳庣叅闁哄稁鍘介悡渚€鏌涢妷锝呭缂佺娀绠栭弻鐔衡偓鐢告櫜缁辫櫕銇勮箛鎾跺闁逞屽墯閻楃姴鐣锋總绋款潊闁靛浚婢佺槐鍐测攽閻愯埖褰х紒鑼櫕缁顓奸崱娆樻锤闂佺粯鍔楅崕銈夋偂閺囩喓绠鹃柟瀛樼箓閼稿綊鏌h箛銉хМ闁哄被鍔岄埥澶娾枎閹寸姷鍘滈梻浣告惈婢跺洭宕滃┑鍡╁殫闁告洦鍓涚弧鈧梺鍛婃处閸嬫帡寮抽妷鈺傗拻濞达絽鎲¢崯鐐烘煛鐏炶濮傞柟顖氼樀閹虫牠鍩℃担鍝ヤ喊婵$偑鍊栭幐鍫曞垂閸︻厾涓嶉柧蹇e亗缁诲棝鏌曢崼婵嗩伀闁告柨绉归弻娑㈠Χ閸滀焦鈻堝┑顔硷攻濡炰粙鐛幇顓熷劅闁挎繂娲ㄩ弳銈嗕繆閻愵亜鈧呯磽濮樿泛纭€闁告劘灏欓弳锕傛煙閻楀牊绶查梺鍗炴喘閺岋繝宕堕埡浣囥垻鎲搁弶鍨伃婵﹥妞介獮鏍倷閹绘帒顫戦梻浣告啞閺屻劎绮旇ぐ鎺戞槬婵炴垯鍨圭粻鎶芥煙閹碱厼骞橀柛鐐垫暬閹嘲顭ㄩ崟顓犵厑缂備礁鍊哥粔鎾煘閹寸姭鍋撻敐搴樺亾椤撱劎鐣甸柡灞剧洴瀵挳濡搁妷褌绱橀梻浣芥〃缁€渚€宕幘顔艰摕闁哄浄绱曢悿鈧繝鐢靛Т閸婃悂鍩涙径鎰拺闁革富鍘介悞鍨瑰搴″婵″弶鍔欓獮妯尖偓娑櫭鎾绘⒑閹呯闁硅櫕鎸剧划顓㈡晬閸曨厾锛濇繛杈剧悼閻℃棃宕靛▎鎾寸厽婵°倓鐒﹀畷宀勬煟濞戝崬娅嶇€规洘锕㈤崺锟犲礃閻愵剛銈梻浣筋嚙閸戠晫绱為崱娑樼;闁圭儤鍤﹀☉銏犵闁靛鍨洪弬鈧梻浣虹帛閸旀牕顭囧▎鎾村€堕柨鏂款潟娴滄粓鏌曟繛鍨姕妞ゃ儯鍨婚埀顒冾潐濞叉牠骞栭锕€鐓″鑸靛姇椤懘鏌嶉柨顖氫壕闂佸綊顥撶划顖滄崲濞戞瑦缍囬柛鎾楀啫鐓傞梻浣侯攰椤曟粎鎹㈠┑鍡欐殾妞ゆ牜鍋為崐閿嬬箾閿濆骸鍘哥紒銊嚙椤啴濡堕崱妯烘殫闂佺顑囬崑銈堟"闂侀潧绻嗛幊鍥磻閹捐埖鍠嗛柛鏇ㄥ墰閿涙﹢姊洪崨濠冣拹闁搞劌娼℃俊瀛樻媴缁洘鐎婚梺鍦亾濞兼瑦绂嶅Δ鍛厵闁煎湱澧楄ぐ褏绱掗煫顓犵煓妤犵偞鐗犲畷銊︾節閸曨厾妲囬梻浣圭湽閸ㄨ棄顭囪閺嗏晜淇婇悙顏勨偓褏绱為埀顒佷繆椤愩垹顏╃€规挸瀚板娲川婵犲嫧濮囧┑鐐插悑閻熲晛鐣疯ぐ鎺戠<闁绘劗琛ラ幏濠氭⒑閸撴彃浜為柛鐘虫崌閸┿垽骞樼紒妯煎幐闁诲函缍嗘禍鐐存櫏闂備礁鎼悮顐﹀礉瀹€鍕厴闁硅揪绠戦獮銏ゆ煃閸濆嫬鈧劙鏁冮埀顒勫煘閹达富鏁婃繛鍡欏亾缂嶅牓姊虹紒妯绘儓缂佺粯绻傞锝嗙節濮橆儵鈺呮煃鏉炴媽鍏岄柣顐㈠濮婅櫣绮欓幐搴㈡嫳缂備礁顑嗙敮锟犲箖閻㈠壊鏁傞柛鈩冪懅閿涙繃绻涙潏鍓у埌鐎殿喖鐖奸、鎾诲幢濞戞瑧鍘遍柣搴秵閸嬪懐浜搁銏$厓閻熸瑥瀚悘鎾煙椤旇娅婄€规洖缍婇、鏇㈡晲閸℃瑦顫栧┑鐘垫暩婵敻顢欓弽顓炵獥婵°倕鎳庣粻浼存煕閹邦垰鐨洪柡鍡畵閺岀喖鏌囬敃鈧悘娑樏瑰鍐Ш闁哄瞼鍠栭幃婊兾熺拠鏌ョ€烘繝鐢靛仜閹冲繘鎮ч悩璇茬畺婵°倕鎳愬畵渚€鏌涢…鎴濇灈濠殿喖楠搁埞鎴﹀煡閸℃ぞ绨煎┑顔硷工椤兘鐛幋锕€顫呴柕鍫濇噹閼板灝鈹戦悙鏉戠仸闁荤啙鍥у偍闁汇垻鏁哥壕浠嬫煕鐏炲墽鎳呴柛鏂跨Ч閺屻劌顫濋銏犻叄瀹曞墎鎹勯搹閫涙闂備礁鎼惌澶岀礊娓氣偓閻涱喖顫滈埀顒€鐣峰鈧畷锝嗗緞婵炴儳浜炬い鏍仦閳锋垿姊洪锝囥€掗柍瑙勫浮閺屾盯寮捄銊愩倝鏌熼獮鍨仼闁宠鍨归埀顒婄秵娴滄粎绮e☉姗嗘富闁靛牆妫欑粈鈧梺鐟板暱缁夌懓鐣烽鈶芥棃宕ㄩ瑙勫濠电偠鎻徊浠嬪箟閿熺姴鐤柣鎰劋閻撶喐淇婇妶鍕窗婵炲牊绮撻弻鐔碱敊閵娿儲澶勯柛瀣姉閳ь剛鎳撴竟濠囧窗閺嵮€鏋旈柕濞炬櫆閳锋垿鏌涢敂璇插绩婵$偓鎮傞弻娑㈡偐閹颁焦鐤侀悗瑙勬礃閸ㄥ灝鐣烽悢纰辨晬婵炴垶鑹鹃獮鍫熺節閻㈤潧鈻堟繛浣冲應鍋撳鐓庡⒋鐎规洘绻傞~婵囨綇閳哄喛绱查梻鍌氼煬閸嬫帡宕㈡ィ鍐╁剹婵炲棙鍔栭崣蹇撯攽閻樻彃浜為柣鎾瑰亹閳ь剝顫夊ú妯兼暜閹烘鐓濋幖娣妼缁狅絾绻濋棃娑欙紞闁诲孩娼欓埞鎴︽偐濞堟寧娈扮紓浣介哺濞茬喎鐣烽幋婵冩婵妫涢崝鐑芥⒑閻愯棄鍔氱痪缁㈠弮瀵娊鏁冮崒娑氬帾闂婎偄娲㈤崕宕囧閸ф鈷掗柛鏇ㄥ亜椤忣偆绱掓潏銊ョ闁逞屽墾缂嶅棝宕㈤悾灞惧厹闁割偅娲橀悡銉︾箾閹寸偟鎳呴柟鍐叉处閹便劍绻濋崶鈺冪獥闂侀潧娲﹂崝娆撶嵁閹烘绠奸柛鏇ㄥ幖閹偟绱撻崒姘偓宄懊归崶鈺冪濞村吋娼欑壕瑙勪繆閵堝懎鏆炴い顐f礋閺岋綁骞囬浣瑰創闂佸憡鍔忛崑鎾翠繆閻愵亜鈧牠骞愰悙顒佸弿缁炬儳顑冩禍褰掓煕閺囥劌鐏¢柍閿嬪灴閺岀喖鎳栭埡浣风捕闂佸憡姊归敃銏ゅ蓟濞戙垹妫橀悹鎭掑壉閿濆鐓曢柟鐑樺煀闊剛鈧娲橀〃濠囧箠閺嶎厼鐓涢柛鎰劤閺咁參姊虹拠鍙夋崳闁硅櫕鎸荤粩鐔哥節閸パ呯崶闂佸搫娲㈤崹鍦不閻旇偤鏃堟晲閸涱厽娈查梺缁樻尰缁嬫垿婀侀梺鎸庣箓濞村倿鎮炴ィ鍐╃厓鐟滄粓宕滃▎蹇g劷闁炽儲鍓氶崵鏇㈡偣閸ャ劎銈存俊鎻掔墦閺屾洝绠涢弴鐐愩垻鈧鎸稿Λ婵嗩潖濞差亝顥堟繛鎴d含閸旀悂姊虹粙鍧楀弰濞存粌鐖奸弫鎰版倷閸濆嫮鍘搁梺鍛婂姦娴滅偤鏁嶅┑鍥╃閺夊牆澧界粔顕€鏌¢埀顒佹綇閳哄啰鐒炬繛瀵稿帶閻°劑鎮¢弴銏$厓闁告繂瀚埀顒傜帛閺呭爼顢楅崒婊咃紲閻庡厜鍋撻柛鎰靛枛閹界數绱撴担铏瑰笡缂佽鐗嗛悾鐑藉醇閺囩倣鈺呮煏婢跺牆鐏╁ù婊堢畺濮婃椽宕归鍛壄婵炲瓨绮嶇划鎾绘偂椤愶箑鐐婇柕濠忕畱绾板秴顪冮妶鍛疄闁稿﹥绻堝璇测槈濮橈絽浜鹃柨婵嗛娴滄繄鈧娲栭惉濂稿焵椤掍緡鍟忛柛鐘虫礈閸掓帒鈻庨幘鎵佸亾娴e壊娼ㄩ柍褜鍓熼獮鍐ㄢ枎韫囧﹥鐏侀梺鍓茬厛閸犳寮抽鍫熲拻闁稿本鑹鹃埀顒傚厴閹虫宕奸弴鐐插亶閻熸粍妫冮弫鎰版倷閸濆嫬宓嗛梺闈涚箳婵兘鏁嶅▎蹇婃斀閹烘娊宕愰弴銏犵疇闊洦绋戠壕鎸庝繆閵堝嫯鍏岀紒鐘荤畺閺屾盯鍩勯崗鈺傚灩娴滃憡瀵肩€涙鍘介梺瑙勫劤椤曨參骞婇崶顒佺厸鐎光偓鐎n剛袦濡ょ姷鍋涢澶愬箖濞嗘挸骞㈡俊顖濇娴煎矂姊虹拠鈥虫灀闁逞屽墯閺嬬厧危閸儲鐓忛煫鍥ュ劤绾惧潡鏌涘鈧禍鍫曞蓟閿濆棙鍎熸い鏍ㄧ矌鏍¢梻浣侯焾椤戝懘骞婇幇顓狀洸闁归棿绶¢弫鍥煟閺冨倻绡€缂併劏顕ч—鍐Χ閸℃衼缂備浇灏▔鏇犲垝婵犳碍鍊锋繛锝庡厸缁ㄥ姊洪棃娑氱畾婵℃彃瀚伴幊鎾诲锤濡や胶鍘靛銈嗘椤鈻嶆繝鍕ㄥ亾鐟欏嫭绀冮柨鏇樺灲閻涱噣骞樼拠鑼唺闂佸搫鍊告晶浠嬪极閻愵剛绡€闁汇垽娼у暩闂佽桨绀侀幉锟犲箞閵娾晜鍋ㄩ柛鎾冲级閺呪晠姊洪崫鍕枆闁告鍋愮划锝呂旈崨顔惧幐閻庡箍鍎辨鎼佺嵁濡ゅ懏鐓涢柛娑卞枤缁犵偤鏌$仦鐐缂佺粯鐩畷褰掝敊閻撳寒娼曢梻鍌欑閹碱偊顢栭崨顖滅煋鐟滅増甯掗拑鐔兼煏婵炲灝鍔楅柡鈧禒瀣厱闁斥晛鍙愰幋锕€绠栨繛鍡樻尰閳锋垿鏌熼懖鈺佷粶濠碉紕鏅槐鎺旀嫚閹绘帗娈堕梺鐟扮畭閸ㄥ綊鍩ユ径鎰潊闁绘灏埀顒€鐏濋埞鎴炲箠闁稿﹥娲熷畷顖涘鐎涙ê浠兼俊銈忕到閸燁垶鍩涢幋锔界厱婵犻潧妫楅鎾煕鎼达紕绠绘慨濠呮閺侇噣顢欓崜顬粓鎮楀▓鍨灈妞ゎ厾鍏橀獮鍐閵忕姵鐎抽柡澶婄墑閸斿秴鈻嶉弽顓熲拻濞达綀娅i妴濠囨煕閹惧绠為柕鍡楀暣瀹曘劑寮堕幋鐐剁发婵犵數鍋涘Λ娆撳礉閹寸偟顩叉繝濠傜墛閻撳繐顭跨捄铏瑰闁告柣鍊濆顐﹀醇濠靛啯鏂€濡炪倖姊婚妴瀣啅閵夛负浜滄い鎾跺仜濡插鏌i敐鍥у幋妤犵偞甯¢獮瀣籍閳ь剟鎮楁繝姘拺闁荤喐澹嗛幗鐘电磼鐠囨彃鈧潡鍨鹃弽銊ョ窞闁归偊鍘搁幏娲煟閻樺弶鎼愮€殿喖鐖奸獮鎴︽晲婢跺鍘介梺缁樻⒒椤牓鍩㈤弴鐘亾鐟欏嫭绀冩い銊ワ躬楠炲啴鍩¢崨顔藉劒濡炪倖鍔楁慨鎶芥惞鎼淬劍鈷掑ù锝堝Г閵嗗啰绱掗埀顒佺瑹閳ь剙鐣烽幇鏉块敜婵°倐鍋撶紒鐘崇墵閺岀喖顢涢崱妤佸櫤婵炲牊娲樼换婵嬫偨闂堟刀銏ゆ煕閻斿憡灏︾€殿噮鍋勯…銊╁礃閿濆棙鏉搁梻浣瑰缁嬫垹鈧凹鍓氱粋宥嗙附閸涘﹦鍘辨繝鐢靛Т閸燁垳绮堥崼銉︾厵妤犵偛鐏濋悘鍙夘殽閻愬弶鍠樼€殿喖澧庨幑鍕Ω瑜庨悗顕€姊虹拠鏌ヮ€楃紒鐘茬Ч瀹曟洟宕¢悘缁樻そ閺佸啴鍩€椤掑嫭鍋╅柣鎴f閽冪喖鏌曟径娑橆洭闁告﹢浜跺娲棘閵夛附鐝旈梺鍝ュ枍閸楁娊宕烘繝鍥у嵆闁靛骏绱曢崢杈ㄧ節閻㈤潧孝闁稿﹦绮粋鎺戔槈濮樿京锛滅紓鍌欑劍椤洤煤鐎涙﹩娈介柣鎰▕閸庢棃鏌熼鐣屾噰鐎规洖缍婇、鏇㈠閳藉棔妲愰梻鍌氬€搁崐鐑芥嚄閸撲礁鍨濇い鏍ㄧ矋閺嗘粌鈹戦悩鎻掝仼闁搞劍绻冪换娑㈠幢濡纰嶉梺钘夊暟閸犳牠寮婚妸銉㈡斀闁糕檧鏅滄晥闂備胶顭堥鍛偓姘煎墴閳ユ棃宕橀浣镐壕闁挎繂绨肩花濂告煙閻у摜鍒伴摶鏍煛閸愩劎澧涢柍閿嬪笒闇夐柨婵嗘噺閸熺偤鏌熼姘卞ⅵ闁哄被鍊曠叅閻犲洩灏欐禒顖滅磽娓氬洤鏋熸俊顐㈠暣楠炲啫顭ㄩ崼鐔哄弰闂佺厧澹婇崜娆愪繆閻e瞼纾兼俊銈呭暙閺嬫盯鏌涢埞鎯т壕婵$偑鍊栫敮鎺斺偓姘煎墴閹锋垿鎮㈤崫銉ь啎闂佺懓鐡ㄩ悷銉╂倶閳哄啰纾奸柣妯烘▕閻撳ジ鏌熼鑲╃Ш闁圭厧缍婇幃鐑藉级閸噮鐎遍梻鍌欐祰椤曆呮崲閹扮増鍋嬮柟鐐墯濞兼牠鏌ц箛姘兼綈閻庢碍宀搁弻宥夊Ψ閵婏妇褰ч梺璇茬箰濡繂顫忓ú顏勫窛濠电姴瀛╅悾閿嬬節閻㈤潧浠滈柨鏇ㄤ簼娣囧﹦鈧稒蓱婵绱掗娑欑闁诲骸顭峰铏规喆閸曨偄濮㈤梺鍝ュ枙濞夋洟鎳為柆宥呂ㄩ柨鏂垮⒔閻﹀牓姊洪棃娑㈢崪缂佹彃澧藉☉鍨偅閸愨晝鍘惧┑鐐跺蔼椤曆囨倶閿旈敮鍋撳▓鍨灓妞ゎ厼鐗撻崺銉﹀緞閹邦剦娼婇梺鎸庣☉鐎氼剟鐛澶嬧拻濞达綀娅g敮娑㈡煙缁嬫寧鎲搁柍褜鍓氱粙鍫ュ疾濠靛绠憸鐗堝笚閺呮悂鏌eΟ铏癸紞闁告鏁诲娲川婵犲嫭鍣у銈忛檮婢瑰棙绂嶉幖浣规櫆闂佹鍨版禍楣冩偡濞嗗繐顏紒鈧崼銉︾厱闁绘ê纾晶鐢告煏閸℃洜顦﹂摶鏍归敐鍛喐缂佹劗鍋炵换婵嬫偨闂堟刀銏ゆ煕閻曚礁鐏﹂柟顔炬暬椤㈡宕熼鑺ュ闂備胶顭堥張顒勬嚌妤e啫鐒垫い鎺嶇劍閸婃劗鈧娲橀崝娆撶嵁閺嶃劍濯撮柛婵勫劵缁鳖噣姊绘担铏瑰笡闁搞劌鍚嬮幈銊╁Χ婢跺﹦锛欓梺绉嗗嫷娈曢柣鎾卞劦閺岋繝宕堕埡浣风捕闂侀€炲苯澧柟鑺ョ矌閸掓帗绻濆顒€鍞ㄥ銈嗘尵閸犳捇宕㈤崡鐑嗘富闁靛牆妫楁慨褏绱掗幓鎺戔挃缂侇喖鐗撻崺鈧い鎺戝€荤壕濂告煕閹炬鍟╂竟鏇㈡煟鎼达絿鎳楅柛銉仜閿曞倹鐓曢柡鍥ュ妼閻忕娀鏌涢幇銊ヤ壕濠碉紕鍋戦崐鏍礉閿曗偓椤潡鍩€椤掑倻纾兼い鏃傚帶椤e磭绱掓潏銊﹀鞍闁瑰嘲鎳橀獮鎾诲箳瀹ュ拋妫滃┑鐘垫暩婵即宕归悡搴樻灃婵炴垶鐟ョ欢鐐烘煕閵夘喖澧痪鎯ь煼閺岀喖骞戦幇顒€鎯為悗瑙勬尫缁舵岸寮诲☉鈶┾偓锕傚箣濠靛洨浜┑鐘愁問閸犳牗顨ラ幖浣测偓鏃堝礃椤斿槈褔鐓崶銊︾缂佹劖顨婂娲川婵犲孩鐣堕梺鍝ュ枎濞硷繝骞冩ィ鍐╁€婚柦妯侯槺椤撴椽姊洪幐搴㈢5闁稿鎹囬弻锝夊箻鐎靛憡鍒涢梺鍝勬湰缁嬫垿鍩ユ径鎰闁绘劕顕禍楣冩⒒娴e憡鍟為惇澶岀磼椤旂晫鎳冩い顐㈢箻閹煎湱鎲撮崟顐㈠箲闂備礁鎲℃笟妤呭窗閺嵮€妲堢憸蹇曟閹惧瓨濯撮柣鐔稿缁佺兘姊洪柅鐐茶嫰婢т即鏌涢敐鍐ㄥ姦鐎殿喗濞婇弻鍡楊吋閸″繑瀚介梻浣侯焾閺堫剟鎮疯瀹曟繂顓奸崨顏呮杸闂佺粯鍔橀婊堢叕椤掑倵鍋撳▓鍨灁闁告柨绉撮…鍥疀濞戞鍘搁梺绋挎湰缁嬫帡顢欓崶顒佲拻濞达絽鎲$拹锟犳煕鎼存稑鈧繈濡撮崘顔煎耿婵炲棙鍨崇粭澶愭⒑閸︻厼鍔嬫い銊ユ閸╂盯骞掗幊銊ョ秺閺佹劙宕堕妸銉︾暚婵$偑鍊栧ú妯煎垝鎼达絾顫曢柟鐑樻⒐鐎氭岸鏌熺紒妯哄潑闁稿鎹囧畷绋课旈崘銊с偊濠电姷鏁告慨鎾箠閹扮増鍋柍褜鍓欓埞鎴︽倷閺夋垹浠稿銈庡幖濞差厼顕f繝姘唶闁靛鑵归幏铏圭磽閸屾瑧鍔嶉柨姘攽椤旂⒈妯€闁哄本绋掗幆鏂库槈濡嘲浜炬繝闈涱儏缁犳牠鏌ㄩ悢鍝勑㈤柛妤佸▕閺屾洝绠涢妷褏锛熼梺鍛娒肩划娆忣潖濞差亜浼犻柛鏇ㄥ亐閸嬫捇宕烽娑樹壕缂佹绋戝ú銈囩不濮樿埖鐓曟い鎰剁悼鐠愨晝鎲搁悧鍫濈瑲闁稿鍨块弻娑樷槈閸楃偛瀛e┑鐐叉▕閸樺墽妲愰幘瀛樺濞寸姴顑呴幗鐢告煟閵忊晛鐏i柛瀣枎鍗遍柟鐗堟緲缁犳娊鏌熼崘鑼紞闁哥姵鎸鹃崚鎺楊敇閻樺啿浠掗梺鐐藉劚閸樻牗绔熼弴銏♀拺闁革富鍘奸崝瀣亜閵娿儲顥㈤柟顔光偓鏂ユ瀻闊浄绲剧€靛矂鏌f惔顖滅У濞存粠浜、鎾澄旈崨顕呮闁诲函缍嗘禍璺恒€掓繝姘厪闁割偅绻勭粻缁樹繆缂併垹娅嶉柡宀€鍠栧畷銊︾節閸屾鐏嗛柣搴㈩問閸犳牠鈥﹂悜钘夋瀬闁归偊鍘肩欢鐐烘倵閿濆骸浜濋柣婵囧▕濮婄粯鎷呯憴鍕哗闂佺瀵掗崹璺虹暦濠靛棭鍚嬮柛娑樻噺鐢€崇暦閻旂⒈鏁嶆繛鎴炲笚鐎氬ジ姊婚崒娆戣窗闁稿妫濆畷鎴濃槈閵忊€虫濡炪倖鐗楃粙鎺戔枍閻樼粯鐓曟繛鍡楁禋濡茶泛霉濠婂嫮鐭嬮柕鍥у楠炲洭鍩℃担鍝勫Ф婵犵鈧啿绾ч柟顔煎€块獮鍐晸閻樺弬褔鏌涢埄鍐╃缂佺姵鑹鹃—鍐Χ閸℃瑥顫х紓渚囧枛閻ジ寮鈧畷濂稿即閻斿搫骞堥梻渚€娼ч…顓熶繆閸モ晝涓嶆慨妞诲亾闁哄苯绉烽¨渚€鏌涢幘瀵告噰鐎规洏鍨归…銊╁醇濠靛牞绱遍梻浣烘嚀婢х晫鍒掗鐐村亗闁哄洢鍨洪悡娑㈡煕閵夛絽鍔氬┑锛勫帶闇夋繝濠傛噹娴犻亶鏌$仦鍓р槈闁宠娴锋禒锕傚箣閹烘埈妫滄繝鐢靛Х閺佸憡鎱ㄩ悜钘夋瀬闁告稑锕ラ崣蹇撁归崗鍏肩稇闁搞劌鍊搁埞鎴﹀磼濠婂海鍔搁梺鍝勫閸庣敻寮婚垾鎰佸悑閹肩补鈧磭顔愮紓鍌欒閸嬫挸顭块懜闈涘闁绘挻鐩弻娑㈠Ψ閵娿儳鍘紓浣藉煐缁嬫挾妲愰幘鎰佸悑闁糕剝鐟ラ埛宀勬⒑閸濆嫭婀扮紒瀣灴閸┿儲寰勬繛銏㈠枛瀹曟宕楅悡搴㈢亪闂傚倸鍊烽懗鍓佸垝椤栫偛绠板Δ锝呭暙缁愭鏌熼柇锕€骞橀柍鐟扮Т閳规垿鎮╅崣澶屻偐闂佽桨绀佺粔鐢垫崲濠靛鍨傛い鎰╁灩椤苯鈹戦悙鑼⒈闁告ê澧藉Σ鎰板箻鐎涙ê顎撻梺鑺ッˇ鎶藉极閸噮娓婚柕鍫濇閼茬娀鏌涢妷锝呭闁伙絽鍟块埞鎴︽偐閸偅姣勬繝娈垮枟閹告娊寮崘顔嘉у璺猴功閺屽牊绻涢弶鎴濇倯婵炲吋鐟╁浼村Ψ閳哄倻鍙嗗┑鐘绘涧濡瑩藟閻愮儤鐓曟繛鍡楃箳缁犱即鏌嶇憴鍕伌闁诡喒鏅犻獮鎾诲箳瀹ュ洦鏅奸梻鍌欒兌缁垶骞戞笟鈧畷鎴﹀箛閺夎法鍔﹀銈嗗笒閸犳艾顭囬幇顓犵闁告瑥顦介悞浠嬫煛娓氬洤娅嶆鐐村笒铻栭柍褜鍓熼幃鈥斥攽鐎n亞顔愬┑鐑囩秵閸撴瑦淇婇懖鈺冪<闁绘瑥鎳愮粔顕€鏌$仦璇插闁宠鍨垮畷鍗炍熼搹鍦春闂佽姘﹂~澶娒洪弽顓熷亯闁绘挸瀵掑鏍р攽閻樺疇澹樼痪鎯у悑缁绘盯宕卞Ο铏瑰姼濠碘€虫▕閸o絽顫忛搹瑙勫厹闁告粈绀佸▓婵堢磽娴h櫣甯涚紒璇茬墦閹即顢氶埀顒勭嵁閸ヮ剦鏁囬柣妯兼暩濡插洦绻濆▓鍨灍闁挎洍鏅犲畷銏ゅ礂閼测晩娴勫銈嗘尪閸ㄦ椽宕戦埄鍐瘈濠电姴鍊搁弳鐔虹磼閻樺搫鍚归柍褜鍓濋~澶娒哄Ο铏规殕闁归棿鑳跺畵渚€鏌熼悜妯烘闁哄啫鐗嗛悞鍨亜閹烘垵鈧崵浜搁悽纰樺亾楠炲灝鍔氭い锔垮嵆閹繝寮撮悢缈犵盎闂佽澹嬮弲娑㈠焵椤掍焦绀嬬€殿喖鎲¢幆鏃堝焾鐠鸿櫣绉洪柟顔规櫊閹粌顫滈崱鏇炴憢缂傚倸鍊峰ù鍥ㄣ仈閹间礁绠板┑鐘宠壘缁狀垶鏌涘☉娆愮稇缂佲偓閸儲鐓欑紓浣姑粭鎺戭熆閻熸壆校缂佺粯绻堥幃浠嬫濞戞鎹曟俊鐐€ч梽鍕熆濡厧寮查梻浣虹帛濡啴藟閹捐姹查柨鏇炲€归悡蹇涚叓閸パ屽剰闁逞屽墯閻楃娀骞冮悙鐑樺殐闁宠鍎虫禍鐐殽閻愯尙浠㈤柛鏃€纰嶆穱濠囶敃閵忋垻鍔Δ鐘靛仜缁绘﹢骞栬ぐ鎺戞嵍妞ゆ挾濯寸槐鑼磽閸屾艾鈧兘姊藉澶婂瀭鐟滅増甯炲畵渚€鏌″搴″箺闁绘挻鐟╅弻娑㈠箛椤栨氨姣㈢紓浣哄У濡炰粙寮婚弴銏犵倞闁靛鍎遍~鎴濐渻閵堝繒鐣虫い顐㈩樀楠炲牓濡搁敂鍓х槇闂佺琚崐妤呭触鐎n喗鍊甸悷娆忓缁€鍫ユ煕閻樺磭澧甸柕鍡曠窔瀵挳濮€閻欌偓濞煎﹪姊虹€圭姰鈧偓闁稿鎸剧槐鎺撴綇閵婏富妫冨┑顔硷功缁垶骞忛崨瀛樻優妤犵偛绨遍崑鎾寸節閸ャ劎鍘搁梺鍛婁緱閸犳岸鎯岄幒妤佺厵妞ゆ牗鑹鹃顓熴亜閵忥紕娲撮柟顔界懇濡啫鈽夊銉ヤ喊闂傚倸鍊风粈浣革耿闁秴纾块柕鍫濐槸閸氬綊鏌ㄩ弴鐐测偓鍝ョ尵瀹ュ鐓冪憸婊堝礈閻旇偐宓侀煫鍥ㄧ☉瀹告繈鏌℃径瀣仯缂佸崬鐖煎娲川婵犲啫顦╅梺绋款儏濡繈骞冮崸妤€绀嬫い鎺戝€婚惁鍫㈢磼閻愵剚绶叉い锕佷含婢规洟宕稿Δ浣哄幈闁诲函缍嗛崑鍕倶鐎电硶鍋撶憴鍕闁告梹鐟ラ锝嗙鐎e灚鏅i梺缁樺姈椤旀牕危閻戣姤鈷掑ù锝勮閺€浼存煙濞茶绨界紒顔碱煼楠炲鎮╁顔筋棥闁荤喐绮庢晶妤冩暜濡ゅ懏鍋傛繛鎴欏灪閻撴洟鏌曟径娑氬埌闁告梹宀搁弻锝堢疀婵犲啯鐝氶梺鍝勬湰閻╊垶鐛€n喗鍋愭繛鍫濐儍閸庣敻寮诲鍫闂佸憡鎸婚悷褏鍒掔拠宸悑濠㈣泛锕﹂敍鐔兼⒑閸涘娈樺ù鍏肩箓鐓ゆい蹇撳珋閳哄啯鍠愮€广儱锛嗘径濠庢僵妞ゆ垼濮ら弬鈧梻浣侯焾閺堫剛鍠婂澶婄柈闁绘劗鍎ら悡鐔兼煙閹呮憼缂佲偓閸愵喗鐓忛柛銉戝喚浼冨Δ鐘靛仜濞差厼鐣峰鍕闁间粙鏀遍崹鍦閹烘鍊锋い鎺嗗亾闁告柣鍊栭妵鍕敇閻樻彃骞嬮悗娈垮枛椤兘骞冮姀銈嗗亗閹兼番鍊栭幉浼存⒒娓氣偓濞佳囨晬韫囨稑宸濇い鏃傛櫕濡叉牠姊婚崒姘偓椋庣矆娓氣偓楠炴牠顢曢敐鍛獮闂佹悶鍎洪崜娆撴倿閸偁浜滈柟鍝勬娴滃墽绱掗崜褑妾搁柛娆忓暙椤曪綁骞庨挊澶婅€垮┑鐐村灦閻熴儵鍩€椤掑倹鏆柡灞诲妼閳规垿宕卞☉鎵佸亾濡も偓椤儻顦冲鐟版楠炲啴顢氶埀顒勫极閸岀偛绠i柟鐑樻⒒閻i箖姊绘笟鈧褔鎮ч崱妞曟椽濡堕崨顔界槑闂傚倸鍊烽懗鍫曗€﹂崼銉晞闁搞儺鍓欑壕濠氭煟閺冨倸甯堕柡瀣╃劍閵囧嫰寮村Δ鈧禍鎯旈悩闈涗沪閻㈩垪鈧剚鍤曢柟缁㈠枟閸嬫劙寮堕崼姘珗闁稿繑甯″濠氬磼濮橆兘鍋撻幖浣哥9濡炲娴烽惌鍡椼€掑锝呬壕濡ょ姷鍋涢ˇ鐢稿极閹剧粯鍋愰柤纰卞墻濡茬兘姊绘担鐟邦嚋婵﹤顭峰鏌ヮ敃閿旇 鍋撻崨鏉戠煑濠㈣泛鐬奸惁鍫ユ⒒閸屾氨澧涚紒瀣浮閹繝鍩€椤掑嫭鈷戦柛锔诲幖閸斿銇勯妸銉﹀殗闁诡喗鐟︾换婵嬪礃閿旇法鐩庨梻浣烘嚀閹碱偆绮旈悜绛嬫晩濠㈣埖鍔栭悡娆忣渻鐎n亝鎹i悽顖涚〒缁辨帞绱掑Ο灏栧濠电偟鍘х换妯虹暦濠婂棭妲婚梺绯曟櫅閻倸顫忛搹瑙勫厹闁告粈绀佸▓婵堢磽娴h櫣甯涚紒璇茬墦閹即顢氶埀顒€鐣烽崡鐐╂婵せ鍋撻柛鐐茬埣濮婃椽妫冨☉杈€嗘繝纰樷偓铏枠鐎规洏鍨介獮鏍ㄦ媴閸忓瀚奸梻浣告啞閹告槒銇愰崘鈺冾洸濞寸姴顑嗛悡鏇㈡倵閿濆簼绨绘い蹇d邯閺岋繝宕ㄩ鐘茬厽濡ょ姷鍋涚粔褰掋€佸▎鎾崇鐟滄繄妲愰崣澶夌箚闁绘劦浜滈埀顒佺墪椤繑绻濆顒傛煣濡炪倖鍔х粻鎴犵不閻樼粯鐓曢柕澶樺枤閸樻稒绻涢崼婊呯煓闁哄矉缍侀獮鍥敇閻旇櫣鈻忕紓鍌欑劍椤ㄥ棛鏁敓鐘茬闁割偅娲栭崘鈧銈嗘尵閸犳捇宕㈤幘缁樺仭婵犲﹤瀚惌鎺斺偓瑙勬礃缁矂鍩ユ径濠庢僵妞ゆ巻鍋撻柣蹇擄躬閺岋綁鎮╅崣澶嬫倷濠碘槅鍨伴敃銈夆€﹂崶顒€鐓涢柛娑卞枤閸橀箖姊洪崨濠勭細闁稿孩鐓″鎶藉煛閸涱喚鍘卞┑鈽嗗灣缁垶宕愰幇顓熷弿濠电姴鍟妵婵堚偓瑙勬磸閸斿秶鎹㈠┑瀣<婵ê鍚嬬紞鍡涙⒒閸屾瑧顦﹂柟璇х節瀵濡歌閸嬫挸鈽夐幒鎾寸彋閻庢鍠楅悡鈥崇暦婵傜鍗抽柣鎰絻缁侇噣姊绘担铏瑰笡婵﹨宕甸幑銏犫攽閸絽小闁荤姴娲ゅΟ濠傘€掓繝姘厪闁割偅绻冮ˉ婊冣攽椤旂厧鈧潡寮诲☉銏犖╅柨鏂款潟娴犮垽鎮楃憴鍕闁轰浇顕ч悾鐑藉醇閺囥劍鏅㈡繛杈剧到閹碱偊鐛幇鐗堢厽閹肩补鈧啿杈呴梺绋款儐閹瑰洭骞冨Δ鍛櫜閹肩补鈧剚娼婚梻浣虹《閺呮盯鎳熼鐐┾偓鏃堝礃椤斿槈褔骞栫划鍏夊亾閼碱剙鍤紓鍌氬€风欢锟犲窗濡ゅ懎绠伴柟闂寸劍閸嬧晠鏌i幋锝嗩棄缁绢厸鍋撻梻浣虹帛閸ㄩ潧螞濞嗘垟鍋撻棃娑氱劯婵﹥妞藉畷銊︾節閸愩劎妯傞梻浣告啞閸旀垿宕濆澶嬪剨闁瑰墽绮埛鎺楁煕鐏炴崘澹橀柍褜鍓氶幃鍌氱暦閹邦剛鏆嬮柟鍐诧工缂嶅﹤鐣烽崼鏇ㄦ晢濠㈣泛顑嗗▍鏃堟煟閻斿摜鐭婄紒缁橈耿閻涱噣骞嬮敃鈧~鍛存煏閸繃鍣介柣銈傚亾濠碉紕鍋戦崐鏍垂閻旂厧鐤炬繝濠傛噽閻瑩鏌熸潏鍓х暠闁绘挻锕㈤弻鐔衡偓鐢殿焾琚ラ梺绋款儐閹瑰洭寮幇顓熷劅婵犻潧娲﹀畷鎶芥⒒娴d警鏀板┑顔哄€曠叅闁绘柨顨庡鏍ㄧ箾瀹割喕绨荤紒鐘卞嵆楠炴牗娼忛崜褎鍋ч梺浼欑秮濞佳囧煘閹达箑鐓¢柛鈩冦仦缁ㄥジ姊洪懡銈呮毐闁哄懏鐩幃楣冩倻閽樺宓嗛梺闈涚箚閳ь剙鍘栫花濠氭⒒娴d警鐒剧紒缁橆殜瀹曟垿骞囬弶鍨亶濡炪倕绻愰悧濠囧煕閹达附鐓曢柟鐐綑缁茶霉濠婂嫮绠樼紒杈ㄥ笧閹风娀骞撻幒鍡椾壕闁秆勩仠閳ь兛绀佽灃闁告侗鍙庡濠囨⒑闂堟稓绠為柛銊ヮ煼閺佸秴鈹戠€n偄鈧灚顨ラ悙鑼虎闁告梹宀搁弻鐔兼惞椤愩垹顫嶉梺鍝勬噹閻栫厧顕i幘顔碱潊闁挎稑瀚敮妤呮⒑閼姐倕鏋戦柣鐔村劤閳ь剚鍑归崜鐔煎箖濮椻偓楠炴﹢顢欓悾灞藉箥婵$偑鍊栧濠氬疾椤愶箑绠犻柛銉厛濞堜粙鏌i幇顒傛憼鐎规洖鏈〃銉╂倷閺夋垶璇為悗娈垮櫘閸o絽鐣锋總绋款潊闁绘ɑ顔栧Σ鍫曟⒒閸屾艾鈧悂宕愰幖浣哥9闁绘垼濮ら崐鍧楁煥閺冨牊鏆滈柛瀣尵缁厼鈽夊Ο璇叉闂佸搫顑呴悧蹇涘焵椤掆偓缁犲秹宕曢柆宓ュ洭顢涘☉杈ㄦ暞闂傚倸鍊风粈渚€骞夐垾瓒佹椽鏁冮崒姘€繝闈涘€婚…鍫ュ几娓氣偓閺屾稑鐣濋埀顒勫磻閻愮儤鍋傞柡鍥ュ灪閻撴盯鏌涢妷锝呭姎濠碉紕鍘ч湁婵犲﹤瀚粻鏍磼缂佹娲寸€规洖銈搁弫鎰板川椤栨侗鍤勭紓鍌氬€峰ù鍥ㄣ仈閹间礁绠板┑鐘宠壘缁狀垶鏌涘☉鍗炵仯闁活厽鐟╅獮鏍偓娑櫳戠亸顓灻瑰鍫㈢暫闁哄本鐩弫鍌滄嫚閹绘帞顔戦梻浣告惈濡瑧鍒掗幘璇茶摕闁挎繂顦粻娑欍亜閹哄秶鍔嶉柛搴㈡崌濮婅櫣绱掑Ο铏圭懆闂佽绻戝畝鍛婁繆閻㈢绀嬫い鏍ㄦ皑椤斿﹪姊虹憴鍕剹闁搞劎澧楅幈銊モ槈濮樿京锛濇繛杈剧到婢瑰﹤螣閳ь剙鈹戦悙鏉垮皟闁搞儯鍔庨悾鍐测攽閻樺灚鏆╁┑顔芥尦閺佸啴濡堕崶锝呬壕婵鍘ч弸銈囩磼椤旂⒈鐓奸柟顔界懇閹粌螣閻撳骸绠ュ┑锛勫亼閸婃牕顫忔繝姘仱闁哄倸绨遍弸鏃€绻濇繝鍌氼仴濞存粍绮撻弻鏇$疀婵犲喚娼戝┑鐐茬墛缁酣鍩€椤掑喚娼愭繛鍙夌矒瀹曚即寮介婧惧亾娓氣偓瀵粙顢橀悢閿嬬枀闂備線娼чˇ顓㈠磿閻戞ê顕遍柡宥庡幗閳锋帡鏌涚仦鎹愬闁逞屽墴椤ユ挸鈻庨姀鐙€娼╂い鎺戭槺閸旂兘姊洪悡搴綗闁稿﹥鍔欏畷鎴﹀箻缂佹﹩妫冨┑鐐村灦濮樸劑宕濋鐐村€甸悷娆忓绾炬悂鏌涢妸銊︻仩缂傚倹鎸荤粋鎺斺偓锝庝簽椤旀劙姊虹紒妯哄闁哄懏绋掔粋宥嗐偅閸愨晝鍘遍悗鍏夊亾闁逞屽墴瀹曟垵鈽夊杈╃劶闂佺鐬奸崑鐐烘偂閻樺磭绠鹃柡澶嬪焾閸庢劖绻涢崨顓熷枠闁哄矉缍侀弫鍐焵椤掑嫭鍋嬮柟鐐墯濞兼牗绻涘顔荤凹妞ゃ儱鐗婄换娑㈠箣閻愬娈ら梺浼欑稻閸庢娊鍩為幋锕€鐒洪柛鎰╁妿缁佺兘鏌f惔銏㈢叝闁告濞婇悰顔界節閸パ咁啋闁荤姴娲﹂悡锟犲极濠婂啠鏀介幒鎶藉磹閹剧粯鍤勯柛顐f礀閸屻劑姊婚崼鐔剁繁婵炴挸顭烽弻鏇㈠醇濠靛浂妫¢梺鎶芥敱鐢繝寮婚敓鐘叉そ濞达綁鏅查崰濠偽旈悩闈涗粶闁挎洦浜滈悾鐑芥偄绾拌鲸鏅i梺缁橆焽椤n喚妲愰懠顒傜=闁稿本鑹鹃埀顒傚厴閹偤鏁冮崒妞诲亾閿曞倸鐐婇柍鍝勫暕缁楀姊虹紒妯哄妞わ絼绮欏畷鎴﹀箻閼搁潧鏋傞梺鍛婃处閸撴盯藝閵夆晜鈷戠紓浣诡焽婢ь亪鏌涘顒夊剱缂佸矁椴哥换婵嬪磼閵堝棙銆冮柣搴″帨閸嬫挸鈹戦悩鎻掓暘闁冲搫鎳忛悡鐔煎箹濞n剙鐒洪柛鐔风箻閺屾盯鎮╁畷鍥f闂佸疇顕х粔鐟邦嚕閹绢喗鍋愰柛鎰絻缁ㄣ儲绻濋悽闈涒枅婵炰匠鍥舵晞闁糕剝绋戠壕濠氭煏婵炵偓娅嗛柍閿嬪浮閺屾盯顢曢妶鍛亖闂佸磭绮幑鍥蓟閿涘嫧鍋撻敐搴濈凹闁革絽缍婇弻宥囨喆閸曨偆浼岄梺璇″枟閻熲晛顕i崼鏇炲瀭妞ゆ梻鍋撻宥夋⒒閸屾瑨鍏屾い顓炵墢閹广垽骞掑Δ鈧壕濠氭煙閹冾暢闁活厽鐟╅弻鐔告綇閸撗呮殸闂佺粯鎸荤换鍫ョ嵁閺嶎灔搴敆閳ь剚淇婇懖鈺冪<闁绘ê妯婇悡濂告煛瀹€鈧崰鏍嵁閸℃稑绾ч柛鐔峰暞閹瑰洭寮婚妸銉㈡婵炲棙蓱閻h偐绱撴担浠嬪摵闁圭懓娲ら悾鐑藉箳閹存梹鐎婚梺瑙勬儗閸樺€熲叺婵犵绱曢崑鎴﹀磹閺嶎厼鍨傞梻鍫熷厷濞戞ǚ鏀介悗锝冨妷閸嬫挻绗熼埀顒€顕i崐鐕佹Х闂佸搫顑呴柊锝夊蓟閻斿吋鍊锋い鎺嶈兌缁嬪洦绻涚€涙鐭嬬紒顔芥尭椤繘鎼归悷鏉款嚙闂佸搫娲ㄩ崑娑㈠煕婢跺瞼纾藉ù锝呭閸庢劙鎮介妞诲亾瀹曞洦娈鹃梺纭呮彧缁犳垿鎮炲ú顏呯厱闁规澘鍚€缁ㄨ姤銇勯弮鈧ú鐔奉潖閾忕懓瀵查柡鍥╁仜閳峰顪冮妶鍐ㄥ闁绘绻掗崚鎺撶節濮橆厼浜遍梺鍓插亝缁嬫劗鑺辨繝姘棅妞ゆ劑鍨虹粊顐ょ磼閼艰泛浜归柤娲憾閹儳鐣濋埀顒傚婵傜绾ч柛顐g☉婵″吋绻涢幖顓炴珝闁哄本鐩崺鐐哄箚瑜屾竟鏇炩攽閿涘嫬浜奸柛濠冪墱閺侇噣骞掗弬鍝勪壕婵鍘ф晶鎾煙椤旀儳浠辩€规洖缍婇、鏇㈡偐鏉堚晝娉块梻鍌欑濠€閬嶅磿閵堝鍨傞柣銏犲閺佸倹銇勮箛鎾跺闁绘挸鍟村娲垂椤曞懎鍓伴梺璇茬箲閹告娊寮婚悢纰辨晩缂佹稑顑嗛悿渚€鎮楃憴鍕闁稿繑锕㈤妴浣割潨閳ь剟骞冨鍫濆耿闊洦鎸锋竟鏇㈡煟韫囨洖浠滃褏鏅划缁樸偅閸愨晝鍘遍棅顐㈡处濞叉牜鏁捄琛℃斀妞ゆ棁鍋愭晥闂佸搫鐭夌槐鏇熺閿曞倸绀堢憸搴ㄥ礆濞戞瑧绡€缁剧増锚婢ф煡鏌熼鐓庘偓瑙勭┍婵犲洦鍊婚柤鎭掑劜濞呭洭姊洪柅鐐茶嫰婢ь垳绱掗崒娑樻诞鐎殿喖鐖奸獮濠囨惞椤愶綆妫冮梺璇″枓閺呯姴螞閸愩劉妲堟俊銈呭暞瀹曠喖姊婚崒娆戭槮闁硅姤绮撳畷鎶藉Ψ閳轰胶锛涙繝鐢靛Т濞层倝寮伴妷鈺傜厪闊洤锕ゆ晶鏌ユ煕鎼达絽鏋涢柡灞炬礃缁绘盯宕归鐓幮戞俊鐐€栧鍦暜閳ユ剚娼栨繛宸簻娴肩娀鏌涢弴鐐典粵閺佸牓姊绘担瑙勫仩闁告柨鐭傞幃銉︾附閹肩偐鍋撴担鑲濈喖鎳栭埡鍐跨床婵犵妲呴崹鏉匡耿鏉堚晝涓嶆慨妯垮煐閳锋垹绱撴担濮戭亝鎱ㄩ敃鈧湁婵犲﹤瀚惌鎺楁煕閳规儳浜炬俊鐐€栫敮濠囨嚄閼稿灚娅犳い蹇撴噷娴滄粓鏌¢崒婵囩《缂佺姾灏欑槐鎺旂磼濡偐鐣靛銈庡亝缁诲牓銆佸Δ鍛<闁挎梹鍎抽懓鍧楁⒒閸屾艾鈧绮堟担闈╄€块梺顒€绉寸壕濠氭煙閸撗呭笡闁稿鏅滈妵鍕疀閹炬潙娅у銈傛櫅瀵墎鎹㈠┑鍥╃瘈闁稿本绮岄·鈧梻浣虹帛閹稿爼宕曢懠顒佸床婵犻潧顑嗛ˉ鍫熺箾閹寸偟鎳愭俊顐熲偓鎰佹富闁靛牆鍟崝銈夋煕鐎c劌鈧繂顕f繝姘嵆闁靛繒濮烽崐鐐烘⒑闂堟丹娑㈠川椤栨稒鐦掗梻鍌氬€风欢姘跺焵椤掍胶銆掗柍瑙勫浮閺屾盯寮捄銊愩倝鏌熼獮鍨仼闁宠鍨归埀顒婄秵娴滄粎绮e☉姗嗘富闁靛牆妫欑粈鈧梺鐟板暱缁夌懓鐣烽鈶芥棃宕ㄩ瑙勫濠电偠鎻徊浠嬪箺濠婂懐鐭撻柣鎴炃滄禍婊堟煏婢舵盯妾悘蹇斿缁辨帞绱掑Ο鍏煎垱闂佺硶鏂侀崑鎾愁渻閵堝棗绗掗悗姘煎弮閹€斥枎閹存柨浜鹃悷娆忓缁€鈧┑鐐茬湴閸婃繈宕洪姀銈呴唶闁绘梻绻濈花濠氭⒑闂堟稓绠氭俊鎻掓噹閳绘挸顭ㄩ崨顏勪壕閻熸瑥瀚粈鍐偨椤栨澧插ǎ鍥э躬瀹曞ジ寮撮悙鑼崺婵$偑鍊栧Λ浣规叏閵堝鍎婇柡鍐ㄥ€荤壕浠嬫煕鐏炴崘澹橀柍褜鍓氶幃鍌氱暦閹版澘绠瑰ù锝呮憸閿涙瑩姊鸿ぐ鎺擄紵缂佲偓娴e搫顥氶柛锔诲幐閸嬫捇鎮烽弶娆句痪闂侀潻绲块ˉ鎰板Φ閹版澘绠抽柟瀵稿Т閳ь剛鍋涢—鍐Χ閸℃鐟ㄥ銈忕細閸楀啿顕i弻銉晜闁割偆鍠庢禒顓炩攽閻樿宸ラ悗姘煎弮钘熼柛顐ゅ櫏濞堜粙鏌i幇顓炵祷闁哄棎鍨洪妵鍕晝閳ь剙锕㈤柆宥呯劦妞ゆ帒鍠氬鎰箾閸欏澧柣锝囧厴椤㈡宕熼銈呭绩濠电姰鍨煎▔娑㈩敄閸℃瑧绀婇柛銉墯閻撳繐鈹戦悩鑼婵$虎鍣i弻锝呪攽閸曨偄顫囧┑顔硷工椤嘲鐣烽幒鎴旀瀻闁瑰瓨绻傞‖澶愭⒑鐠囧弶鎹i柣鐔稿▕瀹曘劑顢欓悡搴e搸闂傚倷鑳堕…鍫ュ嫉椤掑嫷鏁嬮柕蹇曞Υ濞差亶鏁傞柛鏇炵岸閺呯娀寮诲澶婁紶闁告洦鍋€閸嬫捇骞栨担鍝ヮ槶闂佽崵鍠愭竟瀣绩娴犲鐓熼柟閭﹀墮缁狙勩亜閵壯冧槐闁哄瞼鍠撶划娆撳箰鎼淬垹鏋戠紓鍌欑贰閸犳危閹烘桅闁圭増婢樼粻鎶芥煙閻愵剚鐏遍柛瀣崌瀹曞綊顢曢妶鍥跺晭闂備胶鎳撻顓㈠磿閹邦厼顕遍柛鈩冪⊕閻撴瑩鎮楅悽娈跨劸鐏忓繘姊虹紒妯虹瑨闁挎洦浜濠氭晲閸涘倹妫冮崺鈧い鎺戝閸嬪鏌涢弴銊ュ妞も晛寮剁换婵囩節閸屾凹浠存繛瀛樼矋缁捇寮婚悢鐓庣闁惧浚鍋呴悵鏃堟⒑鐠囧弶绂嬮柛鐘冲哺閸┾偓妞ゆ帊鑳堕埊鏇犵磼鐠囪尙澧曟い顐㈢箻閹煎綊宕楁径濠佸闂侀潻瀵岄崢濂割敁鐏炲墽绠鹃柛蹇曞帶婵秹鏌$仦鍓ф创濠碘剝鎮傛俊鐑芥晝閳ь剚绂掗弶鎳虫棃鎮╅棃娑楃捕闂佸摜鍣ラ崑濠囧春閵忊剝鍎熼柕濞垮劤椤旀帡鎮楃憴鍕婵炲眰鍔戝畷銏ゎ敆閳ь剟鍩為幋锔藉亹妞ゆ棁鍋愭导鍥⒑缁洘娅嗛柣妤冨仱楠炴顢曢姀鈺傚瘜闂侀潧鐗嗛崯顐﹀礉閻㈢數纾奸柤鑹板煐绾埖淇婇崣澶婂妤犵偞顭囬幏鐘绘嚑椤掑﹦搴婂┑鐘垫暩閸嬫稑螞濞嗘挸鏄ラ柛顐f儕閿濆鏁婄痪鎷岄哺鐎靛矂姊洪棃娑氬缂佺粯鍔欓幆浣割煥閸喓鍘遍梺闈涱焾閸斿秹鎮甸鍡欑<闁哄啫鍊搁弸娑氣偓娈垮枟閹歌櫕鎱ㄩ埀顒勬煃閸濆嫬鈧懓鈻嶅澶嬧拻濞撴埃鍋撴繛浣冲懏宕查柛鈩冪☉閻掑灚銇勯幒鎴濇殲闁绘繍浜弻锝夊Χ閸涱喖娈楀┑顔硷攻濡炶棄鐣烽锕€绀嬮柛顭戝€i敃鍌涒拺缂備焦锕╁▓鏃堟煕閻斿憡缍戞い鏇秮楠炴捇骞掑┑鍫濆汲闂備礁鎲℃笟妤佺濠婂嫮顩查柣鎰靛墯閸欏繑鎱ㄥΔ鈧Λ妤呯嵁濡ゅ懏鐓熼柕濠忕畱閻忔挳鏌$仦鐣屝ユい褌绶氶弻娑㈠箻鐎靛憡鍒涘Δ鐘靛仜閿曨亪鐛Ο灏栧亾闂堟稒鎲哥憸鎵亾缁绘繈鎮介棃娴躲垺绻涚仦鍌氣偓妤冨垝閿濆憘鏃€鎷呮搴g暰闂備線娼ч悧鍡涘箠鎼淬劌姹插┑鐘叉处閻撴洟鎮楅敐搴′簼鐎规洖鏈穱濠囶敃閵忕姵娈梺瀹犳椤︻垶锝炲┑瀣闁绘劖鐣悢灏佹斀闁绘ɑ鍓氶崯蹇涙煕閻樺磭澧甸柡浣稿暣婵$兘濡烽钘夌槣闂備浇濮ら敋闁挎稑顦埥澶愬閻樻妲伴梻渚€娼ч…鍫ュ垂濞差亷缍栫€广儱鎳夐弨鑺ャ亜閺冣偓閺嬬粯绗熷☉銏$厱闁瑰灝瀚悾鐢碘偓娈垮枟婵炲﹪銆侀弴銏℃櫜闁搞儮鏅濆Σ鍥╃磽娴g鈷斿褎顨夐幗顐㈩渻閵堝骸浜滈柨鏇ㄤ邯瀵鈽夊锝呬壕闁挎繂绨肩花濂告煕閵堝懏鍠橀柡宀€鍠栭、娆撴倷椤掑倸濮芥俊鐐€х粻鎴犲椤撶姵顫曢柟鐑橆殔绾惧吋鎱ㄥΟ鑽ゆ▊鐟滃酣銆冮妷鈺傚€烽悗鐢殿焾椤呯磽娴h娈橀柛鐘崇墪閻g兘宕奸弴鐐嶁晠鏌ㄩ弮鍌涙珪鐟滄澘妫濆濠氬磼濮橆兘鍋撴搴g焼濞达絽婀遍悵璺衡攽閻樺弶鎼愮痪鎯ь煼閺屾盯鍩勯崘顏佹缂備焦鍔栭〃濠囧蓟閻旂厧绠查柟浼存涧濞堫參姊虹粙鑳潶闁告梹鍨甸~蹇撁洪宥嗘櫌闂侀€炲苯澧扮紒顔芥閹晫绮欑捄銊ュ箞闂備胶顢婇幓顏堟⒔閸曨垰鐓曢柟鐑橆殕閻撴洘銇勯幇鈺佲偓鏇㈠几瀹ュ洨纾奸柛顐f磻閹查箖鏌″畝瀣М妤犵偞鐟╁畷姗€濡搁妷褏娼夊┑鐘愁問閸犳牠鏁冮妶澶嗏偓锕€鐣¢幍顔芥闂佺粯姊婚埛鍫ュ极閸愵喗鐓忛煫鍥э攻濞呭啰绱掓潏銊︾叆闁宠鍨块幃鈺佲枔閹稿孩顔囩紓鍌欒兌缁垳鎹㈤崒鐐┾偓锕傚炊椤忓秵鈻岄梻浣虹《閺呮繈宕戦妶澶屽祦閻庯綆鍠楅弲婵嬫煃瑜滈崜鐔煎蓟鐎n喖鐐婇柕濠忕畱瀵灝鈹戦绛嬫當婵☆偅顨婂畷銏㈢矙濞嗗墽鍞甸柣鐔哥懃鐎氼厾绮堥埀顒勬⒑鐎圭媭娼愰柛銊ユ健楠炲啫鈻庨幘鏉戞濡炪倖宸婚崑鎾淬亜閿濆棙銇濇慨濠呮閹风娀鎳犻鍌ゅ敼缂傚倷娴囬褔宕愰崸妤€鏄ラ柕蹇曞閸氬鏌涘鈧悞锕€顕欏ú顏呪拺闂侇偆鍋涢懟顖涙櫠鐎电硶鍋撳▓鍨灕妞ゆ泦鍥х叀濠㈣泛顭鈺呮煥濠靛棙鍣稿瑙勬礋濮婃椽骞愭惔锝囩暤缂備降鍔岄妶鎼佺嵁閸愵煈鍚嬮柛銉到娴滈箖鎮峰▎蹇擃仾闁稿濞€閺屾稒鎯旈敐鍡樻瘓閻庢鍠栭…鐑藉极閹邦厼绶為悗锝庡亝閻濇娊姊绘担瑙勫仩闁稿孩绮撳畷姗€濡歌閸氬懘姊婚崒姘偓宄懊归崶褜娴栭柕濞炬櫆閸婂潡鏌ㄩ弴鐐测偓鍝ョ不閺屻儲鐓曢柕澶樺枛婢ь喚绱掗悩宕囧⒌闁哄苯绉瑰畷顐﹀礋椤掆偓濞咃絿绱撴担鎻掍壕闂佸憡鍔忛弲婵堢不妤e啯鐓涘璺侯儏閻掗箖鏌涙惔锛勭闂囧绻濇繝鍌滃ⅱ闁伙絾妞介弻鈥崇暆鐎n剛袦濡ょ姷鍋涢澶愬极閹版澘宸濋柛娑卞枟瀹曞矂鏌″畝瀣М妤犵偞顭囬埀顒佺⊕椤洭藝娴煎瓨鈷戦柛婵嗗閻忛亶鏌涢悩宕囧⒌闁绘侗鍠栭鍏煎緞鐎n偄鍔掓俊鐐€栭崝褏寰婇懗顖樹汗闁告侗鍘搁弨浠嬫煟濡澧柛鐔风箻閺屾盯鎮╁畷鍥р拰閻庤娲橀崝娆忕暦缁嬭鏃堝焵椤掑嫭瀚呴柣鏂挎憸缁犻箖鏌熺€电鈧垵顫濈捄鍝勫殤闁瑰吋鐣崝搴ㄥ矗閹剧粯鐓曢柕澶涚到婵′粙鏌熼姘仼闂囧鎮樿箛鏃傚ⅹ濞存粓绠栧濠氬磼濮橆兘鍋撴搴㈩偨婵娉涢悞鍨亜閹烘垵鈧憡绂掑鍫熺厾婵炶尪顕ч悘锟犳煛閸涱厾鍩g€规洩绲惧鍕醇濠婂懐娉垮┑锛勫亼閸婃牠宕濋幋锕€鏄ラ柛鏇ㄥ€犻敐澶婄濞达絿鎳撴禍妤呮⒑闂堟稓澧曟俊顐g懇瀹曪綀绠涢弬鍓х畾闂佺粯鍔欓·鍌炲吹濞嗗緷鐟邦煥閸垻鏆梺璇″枟椤ㄥ牓骞夐幘顔肩妞ゆ帒鍋嗗Σ鐗堢節閻㈤潧浠滅€殿喖鐖奸垾锕傚炊閳哄啰锛濋梺瑙勫劤椤曨參銆呴悜鑺ュ€甸柨婵嗙凹缁ㄨ崵绱掗妸锝呭姦闁哄瞼鍠栭幃鈩冩償閿濆棙鍠栫紓鍌欑椤戝棝宕归崼鏇炵疄闁靛ň鏅涚壕鍏肩節瑜庨崕铏妤e啯鍋℃繛鍡楃箰椤忣亞绱掗埀顒勫礃椤旇棄浠哄銈嗙墦閸婃寮ч埀顒€螖閻橀潧浠滈柛鐕佸亰閸┿垺鎯旈妸銉ь啋閻庤娲栧ù鍌炲疮閸ャ劋绻嗛柣鎰典簻閳ь剚鐗犻獮鎰偅閸愩劑妫烽梺闈涱槶閸庢瑥鈽夐姀鐘茬獩濡炪倖鎸荤粙鎺楀棘閳ь剟姊绘担鐟邦嚋缂佸鍨归埀顒佸嚬閸撴氨绮嬪鍡欓檮闁告稑锕﹂崢杈ㄧ節閻㈤潧孝闁哥喓澧楅弲鍫曟焼瀹ュ棛鍘告繛鎾磋壘濞层倕鈻嶅鍡╂闁绘劖娼欑粭鎺撱亜椤忓嫬鏆欓柍瑙勫灴瀹曞崬螣閻戞浜峰┑锛勫亼閸婃垿宕归搹鍦煓闁硅揪绠戦悡鈥愁熆鐠哄彿鍫ュ几鎼淬劍鐓欓梺顓ㄧ畱閺嬫稑鈹戦悙鍙夋悙闁宠鍨块弫宥夊礋椤愨剝婢€闂備胶顭堥敃銉╂偋閻樿绠栫憸宥堢亙闂佸憡鍔︽禍鐐烘偂閹剧粯顥婃い鎰╁灪婢跺嫭鎱ㄦ繝鍌ょ吋闁靛棗鎳樺畷锝嗗緞瀹€鈧惁鍫熺節閻㈤潧孝闁稿﹦绮弲璺衡槈閵忥紕鍘介梺瑙勫劤绾绢厾绮绘导瀛樼厓閻熸瑥瀚悘鎾煙椤旇娅婇柟宕囧█椤㈡宕掗妶鍛毌闂傚倸鍊风粈渚€骞夐敍鍕殰濠电姴娲ょ涵鈧梺瑙勫劶濡嫰鎷戦悢鍝ョ闁瑰瓨鐟ラ悘鈺冪磼椤愩垻效闁哄瞼鍠栭獮鍡氼槻妞わ絾濞婇弻锟犲幢閹邦兘鍋撳┑鍡╂綎婵炲樊浜滄导鐘绘煕閺囥劌骞樺ù鐓庢喘濮婃椽宕妷銉愶綁鏌eΔ鍐ㄢ枅濠碘€崇摠閹峰懐鍖栭弴鐔衡偓濠氭⒑閸︻厼浜炬繛鍏肩懄缁傛帗绺介崨濠勫幗闂婎偄娲﹀ú鏍ㄧ閿曞倹鐓曢幖绮光偓铏瘣闂佸疇顕х粔鎾綖濠婂牆鐒垫い鎺嗗亾妞ゎ偄绻掔槐鎺懳熼懖鈺傚殞闂備線鈧偛鑻晶鎾煕閳规儳浜炬俊鐐€栫敮鎺楀磹閸涘﹦顩锋繝濠傜墛閻撶姵绻涢懠棰濆殭闁诲骏绻濋弻锟犲川閺夎法鍘柣搴濈祷閸嬫劙鍩€椤掍胶鈯曟い顓炴喘瀹曘垽宕ㄦ繝鍕啎闁哄鐗嗘晶鐣岀矓椤掍降浜滄い鎰╁焺濡偓閻庤娲橀崝娆撶嵁閸ヮ剚鍋嬮柛顐犲灩鐢姊绘笟鈧褔藝娴犲鍨傞柟鎯板Г閸嬧晠鏌i姀銏╂毌闁稿鎸鹃幉鎾礋椤掑偆妲梻渚€娼ч悧鍡涘箟閳╁啰鈹嶅┑鐘叉处閸婅崵绱掑☉姗嗗剱闁哄拋鍓欓埞鎴︽偐鐠囇冧紣闂佺懓鍟块ˇ顖濈亱闂侀潧艌閺呮粓鍩涢幋锔界厾濠殿喗鍔曢埀顒佹礋瀵悂骞嬮悩鐢碉紲濡炪倖妫侀崑鎰櫏闁诲孩顔栭崰鏍€﹂柨瀣╃箚闁归棿绀侀悡娑㈡倵閿濆骸澧伴柍绗哄€濆缁樼節鎼粹€茬盎濠电偠顕滅粻鎾荤嵁韫囨洍鍋撻敐搴樺亾閵忊剝銇濇い銏℃煥椤撳ジ宕卞Ο鑽ゅ絾闂傚倸鍊风粈渚€骞夐埄鍐懝婵°倕鎳庨崒銊︾箾瀹割喕绨奸柛瀣ㄥ妼閳规垿鎮╁畷鍥舵殹闂佹娊鏀辩敮鎺楁箒闂佹寧绻傞幊蹇涘疮閻愮儤鐓欐い鏍ㄦ皑婢ф盯鏌曢崶褍顏柡浣稿€块幐濠冨緞濡椿妫嗛梻鍌欑窔閳ь剛鍋涢懟顖涙櫠娴煎瓨鐓熼柣鏃傤焾閳绘洜鈧娲樼敮鎺椻€﹂妸鈺佺妞ゆ帒顦扮紞鍌炴⒒閸屾艾鈧悂宕愰幖浣哥9闁归棿绀佺壕褰掓煙闂傚顦︾痪鎯х秺閺岋綁骞嬮敐鍛呮捇鏌涢妶鍛伃闁哄本鐩、鏇㈡晲閸℃瑱绱梻渚€鈧偛鑻崢鎼佹煟閹虹偛顩柟骞垮灩閳规垹鈧綆浜為敍婊冣攽鎺抽崐鎾绘嚄閸洖鐒垫い鎺嶇劍閵囨繃鎱ㄦ繝鍐┿仢鐎规洦鍋婂畷鐔碱敆閳ь剟宕戝澶嬧拺闁硅偐鍋涙俊鑺ヤ繆閻愯埖顥夋い鏇秮瀵濡烽鑺ユ珕闂備礁澹婇崑鍡涘疮閸ф绠紓浣诡焽缁犻箖寮堕崼婵嗏挃缂佸鍠楅妵鍕Ψ閿旇棄闉嶇紓浣割儏椤︾敻骞婇悩娲绘晢闁稿本绮g槐鏌ユ⒒娴e憡璐$紒顕呭灣閺侇喖螖閸涱厾锛涢梺闈涳紡閳ь剟宕戦幘鑸靛枂闁告洦鍓涢ˇ銊ヮ渻閵堝啫濡奸柟铏耿閺佹劙鎮欏顔惧弳闂佸壊鍋呯换鍕礉閿曗偓椤啴濡堕崱妤冪懆闁诲孩鍑归崜婵堟崲濮橆兘鏀介柣鎰摠鐏忎即鏌涢埡浣告殻鐎规洘鍨块獮姗€宕瑰☉妯瑰濠电偛鐗嗛悘婵嬪几閻斿吋鐓欐慨婵嗘湰閻濐亪鏌熸笟鍨闁糕斁鍋撳銈嗗笒鐎氼參鎮¢崘顔界厓閺夌偞澹嗛ˇ锕傛煛閸℃瑥浠遍柡宀嬬到閳规垿宕堕埡浣叉嫲婵犳鍠栭敃锔惧垝椤栨粎绠旈柣鏃傚帶閻掑灚銇勯幒鎴濐仼闁绘帒鐏氶妵鍕箳閹存績鍋撻崨濠勵浄婵犲﹤鐗婇悡鐘崇箾閼奸鍤欓柣蹇ョ節閺岋繝宕ㄩ鐘茬厽濡炪們鍨哄畝鎼佸春閳ь剚銇勯幒鎴濐仼闁藉啰鍠栭弻宥夊煛娴e憡娈堕梺鑽ゅ枎缂嶅﹪寮诲☉銏犖ㄩ柟瀛樼箓椤忣偆鎲搁弶鍨劉缂佺粯绻傞埢鎾诲垂椤旂晫浜梻浣瑰濞测晜淇婇崶顒€绀嗛柟鐑橆殢閺佸秵绻濇繝鍌涘櫧闁伙絽鐖煎铏圭磼濡儵鎷婚梺鍛婎焼閸ャ劌鈧潡鏌涢…鎴濅簴濞存粍绮撻弻鐔煎传閸曨剦妫炴繛瀛樼矋閸庢娊鈥旈崘顔嘉ч幖绮光偓宕囶啇婵犵數鍋炵粊鎾疾閻樼儤顥ら柣鐔哥矌婢ф鏁Δ鍐e亾閻㈤潧校缂佺粯绻堝Λ鍐ㄢ槈濞嗗繐浜跺┑鐐茬摠缁秶鍒掗幘璇茶摕闁绘梻鍘х粻姘辨喐瀹ュ鍤嬬憸鐗堝笚閻撶喖鐓崶褝鏀绘繛鍛喘閺岋綁濡烽濠氬仐濡ょ姷鍋涘Λ婊埶囬幎鑺ョ厱閻庯絻鍔岄崝锕傛煛鐏炵硶鍋撳畷鍥ㄦ畷闂侀€炲苯澧寸€规洑鍗冲鍊燁槾闁哄棴闄勭换婵囩節閸屾凹浠炬繝娈垮灡閹告娊寮婚敐澶婄闁绘劕妫欓崹鍨暦椤栫偛绠虫俊銈勮閹风粯绻涙潏鍓хК濠殿喓鍊濇俊鎾礃椤忓棛锛滈梺閫炲苯澧紒妤冨枛閸┾偓妞ゆ帒瀚弸渚€鏌涢幇闈涙珮闁轰礁鍊块弻娑㈩敃閿濆洨鐣鹃梺纭呭Г濞叉牠鍩為幋锔藉€烽柡澶嬪灩娴犙囨⒑閹肩偛濡块柟铏崌瀵偊顢欓幋鎺旂畾闂佺粯鍔︽禍婊堝焵椤掍胶澧い顐㈢箲缁绘繂顫濋鈧崑宥夋偡濠婂嫭顥堥柡浣瑰姍閹瑦绗熼娑欐珕闂備礁澹婇崑鍡涘疮閸ф绠繛宸簼閳锋垿鎮峰▎蹇擃仼闁告棁娉涢埞鎴︻敊閸濆嫧鍋撳┑鍡╁殨妞ゆ劧闄勯悞鑲┾偓骞垮劚濡绂掗崫鍕垫富闁靛牆妫涙晶锕傛煕婵犲喚娈樼€殿啫鍥х劦妞ゆ帒瀚崐鍨箾閸繄浠㈤柡瀣堕檮閵囧嫰寮撮崱妤佹悙闁绘挴鈧剚鐔嗛悹杞拌閻擃剚绻涚亸鏍ㄦ珕闁靛洤瀚伴獮鍥礈娴g鐓傚┑鐘愁問閸垶宕¢崘宸綎缂備焦蓱婵潙銆掑鐓庣仭闁轰緡鍨伴—鍐Χ鎼粹€茬盎濡炪倧绠撳褔鎮惧畡鎵虫斀閻庯綆浜滃畵鍡涙⒑鐎圭姵纭鹃柟纰卞亰钘濇い鏍仜閻撴﹢鏌熺€电袥闁稿鎹囬弫鎰償閳ヨ尙鐖遍梻浣哥秺閺€鍗烆渻閽樺娼栫紓浣诡焽閻熷綊鏌涢妷鎴濆€婚弫鏍⒒娴d警鐒炬い鎴濇閹嫰顢涢悙鑼枃闂佺粯姊婚埛鍫ュ极瀹ュ棛绠鹃柟瀵稿仧閹冲嫰鏌e┑瀣暠缂佺粯绋撻埀顒傛暩椤牏鏁崼鏇熺厽閹烘娊宕濋幋锕€绠栭柨鐔哄Т閸楁娊鏌曡箛瀣仼鐟滄澘瀚板娲箹閻愭彃濮岄梺鍛婃煥缁夌妫㈤梺鍝勭▉閸樹粙鎮¢悩缁樼厽婵°倐鍋撻柣妤€妫濋、姘煥閸曗晙绨婚梺闈涱煭缁蹭粙宕濋敃鍌涚厵妞ゆ梻鏅幊鍛存煙妞嬪骸鞋妞わ附褰冮湁闁稿繒鍘ф慨宥夋煛鐏炵喎鎳愮壕鍏间繆椤栨粌甯堕柍宄扮焸濮婃椽宕崟顒佹嫳缂備礁顑嗛崹鍧楀春閵夛箑绶為柟閭﹀墰椤㈠懘姊虹紒妯哄閻忓繑鐟╅幆鍫ュ礋椤栨稈鎷绘繛杈剧到閹诧繝骞夐幖浣圭厱閻庯綆鍋嗗ú鎾煙椤斿搫鍔﹂柟顔瑰墲閹棃顢欓悾宀€鈻夊┑鐘垫暩閸嬫稑螣婵犲啰顩叉繝濠傚椤曢亶鏌eΟ鑲╁笡闁绘挻娲熼弻锟犲炊閵夈儱顬堟繝鈷€灞芥灍闁靛洤瀚伴弫鍌滄喆閸曨剛褰嬫繝娈垮枛閿曘儱顪冮挊澹╂盯宕橀妸銏☆潔濠电偛妫楀ù姘i柆宥嗏拻濞达絽鎼崝锕傛煛閸涱亝娅婄€规洝顫夌€佃偐鈧稒锚娴犲ジ姊虹紒妯虹伇婵☆偄瀚划濠氭晲婢跺鍙嗛梺鍝勬处椤ㄥ懏绂嶉崜褏纾藉ù锝呮惈闉嬮悗瑙勬礈閺佺危閹版澘绠婚悗娑櫭鎾绘⒑閸忚偐銈撮柛鎾寸箞瀹曞綊鎮界粙璺ㄥ幒閻庡箍鍎遍ˇ顖炴倷婵犲啨浜滈柟鍝勭Х椤斿鏌熼悿顖涱仩缂佽鲸鎸婚幏鍛村礈閹绘帒澹夐梺璇叉捣閻熸娊宕橀懗顖楀亾閸ф鐓欐繛鍫濈仢閺嬫捇鏌涚€n偅宕岀€规洘顨嗗鍕節娴e壊妫滈梻鍌氬€风粈浣虹礊婵犲伣娑氭崉閵娧呯劶婵炴挻鍩冮崑鎾绘煙閾忣偆鐭庨柕鍥ㄥ姍楠炴帡骞樼捄鍝勭疄濠碉紕鍋戦崐鏍礉瑜忓濠囧礈瑜忛惌鍡涙煕閹伴潧鏋熼柣鎾冲暣濮婃椽宕归鍛壈闂佽绻愰悺銊╁箞閵婏妇绡€闁稿被鍊楅崥瀣倵鐟欏嫭绀€闁靛牊鎮傞獮鍐閵堝懐顦繛杈剧秬濞咃綁鎮鹃崘娴嬫斀闁绘ɑ顔栭弳顖炴煕閹惧绠氶柕鍥ㄥ姍瀹曟﹢顢欓挊澶夊嚱濠电娀娼ч崐濠氣€﹂崼銉﹀珔闁绘柨鎽滅粻楣冩煙鐎电浠ч柟鍐插閺屾稒鎯旈敐鍛亪闂佸搫鏈ú妯兼崲濞戙垹鍨傛い鏃傛嚀娴滈箖鏌″搴″箹缂佹劖顨嗛幈銊ノ熼崹顔惧帿闂佹娊鏀遍崹鍧楀箖瑜版帒鐐婇柨婵嗗€告禍楣冩煣韫囷絽浜炵憸鏉垮缁绘繈鎮介棃娑楃钵闂佸憡鐗滄繛鈧€规洖宕埢搴㈡償閵堝懐鍔靛┑鐘垫暩婵兘寮幖浣哥;闁绘劕鎼粻鏉库攽閻樺疇澹樼紒鈧崟顓熷枑闁绘鐗嗙粭鎺楁煕閵娿儱鈧灝顕i崼鏇為唶婵﹩鍘藉鎺楁⒑缁嬫鍎愰柟鐟版搐铻為柛鎰╁妷濡插牊鎱ㄥΟ鍝勮埞濠殿喛椴哥换婵嗏枔閸喗鐏堥梺鎸庢磸閸庨亶鈥旈崘顔藉癄濠㈠厜鏅滈惄顖氱暦濮椻偓婵℃悂濮€閳藉棙缍屽┑鐘愁問閸犳鏁冮埡鍛闁挎洖鍊稿Ч鍙夈亜閹板墎鎮肩紒鈾€鍋撶紓浣稿⒔婢ф鎽銈庡亜閿曨亪寮诲☉姘e亾閿濆簼绨奸柛銈呮喘閺屾洟宕卞Δ鈧弳锝団偓瑙勬礀閵堝憡鎱ㄩ埀顒勬煟濡灝鐨哄ù婊呭娣囧﹪鎮欓鍕ㄥ亾閺嶎厼绠伴柛顐f礀閸ㄥ倿鏌涢敂璇插箻濞戞挸绉归弻褑绠涢敐鍛暗缂備浇顕уΛ婵嬪蓟閺囥垹閱囨繝闈涙-娴尖偓婵$偑鍊х拋锝囩不閹捐钃熺€广儱鐗滃銊╂⒑閸涘﹥灏伴柣鐔叉櫊楠炲啫螣娓氼垱鍍甸柣鐘荤細濞咃綁鎮块崟顖涒拺闂傚牊渚楅悞楣冩煕鎼淬垻鎳囬柟顔哄灲瀹曟鎮℃惔婵堟殫闂備胶顢婇崑鎰偘閵夆晛鐒垫い鎺戝暙閻ㄦ椽鎮介娑氭创婵﹨娅i幏鐘诲箵閹烘繂濡锋俊鐐€栧褰掓偋閻樿尙鏆﹂柟鍓佺摂閺佸鏌嶈閸撴瑩鎮鹃悜钘夌骇婵炲棛鍋撻崓鐢告煟閻樿崵绱版繛鍜冪秮瀹曟繈鏁冮埀顒勨€旈崘顔嘉ч柛鈩冾殘閻熴劑姊洪崫銉バi柤褰掔畺閳ワ箓宕堕鈧粻娑欍亜閹捐泛啸妞ゆ梹娲熷娲川婵犲嫭鍣у銈冨劘閸ㄤ粙銆侀弮鍫濆耿婵°倐鍋撻柣銈夌畺濮婂宕掑▎鎴М闂佸湱鈷堥崑鍡欏垝濞嗘劗鐟归柍褜鍓欓悾宄邦煥閸愶絾顫嶅┑鐐叉閸╁牆煤缁嬪簱鏀介柣鎰级椤ユ粎绱掔拠鍙夘棦鐎殿喓鍔嶇粋鎺斺偓锝庡亞閸樹粙姊鸿ぐ鎺戜喊闁搞劋鍗抽幃锟犲箛椤旇棄鏋戦梺纭呮硾閿曘倝骞婇幇顔碱棜濠靛倸鎲¢ˉ濠冦亜閹伴潧浜滄鐐达耿閺岋綁顢橀悢鐑樺櫘闂侀€炲苯澧叉い顐㈩槸鐓ら煫鍥ㄧ☉绾惧潡鏌i姀銏╃劸闁哄嫨鍎甸弻宥堫檨闁告挻宀告俊鐢稿礋椤栨氨顔婇梺鐟扮摠缁洪箖宕戦幘缁樺殥闁靛牆鎷嬪Λ婊勭節闂堟稑鈧悂骞夐敓鐘冲亗闊洦鎸撮弨浠嬫煟閹邦垰鐨哄ù鐘灲閺屾盯寮埀顒勫箰閹惰棄钃熼柨婵嗩槸缁犲鏌涢幇顒€绾ч柛濠庡灦濮婃椽鏌呭☉姘f晙闂佸憡鏌ㄧ粔鍫曞箲閵忕姭鏀介悗锝庝簽椤︺劑姊哄畷鍥ㄥ殌闁靛洦锕㈤幖瑙勬償閵婏妇鍘介柟鍏肩暘閸娿倕顭囬幇顓犵閻犲泧鍛殼閻庤娲橀崹鍓佹崲濠靛纾兼繝濠傚椤旀洟姊绘担铏瑰笡婵﹤顭烽崺娑㈠醇閵夈儲鐎梺鍛婂姦閸犳鎮¢妷锔剧瘈闂傚牊绋掗ˉ鐐淬亜閵壯冣枅闁哄备鍓濆鍕節閸曨厜銊モ攽椤旂》宸ユい顓炲槻閻g兘骞掗幋鏃€鐎婚梺鍦劋閸ㄧ數鏁娑楃箚闁绘劦浜滈埀顑惧€濆畷銏$附閸涘﹤浜遍梺鍦亾閻綊鍩€椤戣法绐旂€殿喕绮欓、姗€鎮欓懠鍨涘亾閸喒鏀介柣鎰綑閻忥附銇勯鐐村枠妞ゃ垺鐟╁畷鍫曞Ω閵堝洨鐣鹃梻渚€娼ч悧鍡欐崲閹烘绀嗗ù鐓庣摠閻撴洟鏌i弴姘鳖槮濞存粈鍗抽弻鐔碱敊閹傛閻庤娲栫紞濠囥€侀弴銏″亹閺夊牃鏅濆▔鍧楁⒒閸屾瑧顦︽繝鈧柆宥呯?闁靛牆顦崹鍌炴煟閵忋埄鐒鹃柛鎴犲█閺屾洟宕煎┑鍥舵¥缂備胶濞€缁犳牠寮诲☉婊呯杸闁哄洨鍋涙禒妯荤節濞堝灝鏋涢柣妤€绻掑Σ鎰板箳閺冨倻锛滃┑鈽嗗灠閸氬宕氬☉銏″€甸悷娆忓缁岃法绱掗崣澶婂姢妞ゆ洏鍎靛畷鐔碱敃鐎n剙鏋涢柟顔瑰墲閹棃鍩嶉幒婵呴偗婵﹤顭峰畷鎺戔枎閹搭厽袦婵犵數濮崑鎾绘⒑椤掆偓缁夌敻宕戦妶澶嬬厸闁告劑鍔庢晶鏇犵棯閹规劦鍤欓柍瑙勫灴閹晠骞撻幒宥囨晼婵犵數鍋涢崥瀣偋濡ゅ啯宕叉繛鎴烇供閸熷懏銇勯弮鍥у惞闁告垵缍婂铏圭磼濡櫣顑傜紓渚囧櫘閸ㄦ娊骞戦姀鐘闁靛繒濮烽娲⒑缂佹ê濮岄悘蹇旂懇瀹曟繃瀵肩€涙ǚ鎷洪柡澶屽仦婵粙顢欐径鎰厱閻庯綆鍋呭畷灞炬叏婵犲偆鐓肩€规洘甯掗埢搴ㄥ箣椤撶啘婊堟⒒娴g瓔娼愮紒浣规尦閸┾偓妞ゆ帊绀佹晶顖涚箾閸忚偐澧遍柟鍙夋倐閹囧醇濠靛牏鎳嗛梻浣规偠閸斿矂宕愰崸妤€钃熼柨婵嗩槸椤懘鏌eΟ鍝勬毐闁哄棗鐗撳铏圭矙濞嗘儳鍓梺鍝勬噺缁诲牓宕洪埀顒併亜閹烘垵鈧綊宕甸埀顒勬煟鎼淬垹鍤柛姗€绠栭崺鈧い鎺嶆祰婢规﹢鏌eΔ浣瑰磳妤犵偛鍟存慨鈧柕鍫濇娴滄鏌熼懝鐗堝涧缂傚秴妫楀嵄妞ゆ牜鍋為埛鎺懨归敐鍫燁仩閻㈩垱鐩弻鐔虹矙閹稿孩鍠愰梺閫炲苯澧紒瀣墦瀵彃鈽夐姀鐘靛幒閻庡箍鍎遍幊澶愬绩娴犲鐓曢柍銉ョ-缁犳煡鏌¢崒妤€浜鹃梻鍌氬€烽懗鍓佸垝椤栫偛绀夋慨妞诲亾鐎规洘妞藉浠嬵敄閸欍儲鐫忛柣鐔哥矊缁绘帒危閹版澘绠虫俊銈呭暙瑜板嫬顪冮妶鍡樺暗濠殿喚鍏橀幃锟犲箻濠㈠嫭妫冮幃鈺呮濞戞鍕冩俊鐐€戦崝宀勫箠濮椻偓閸ㄩ箖鏁冮崒姣尖晠鏌嶆潪鎵槮缂佹劖绋戦—鍐Χ閸℃瑥顫х紓渚囧枛闁帮絽鐣烽姀銈嗗亹鐎规洖娲ㄩ惁鍫ユ⒑濮瑰洤鐏叉繛浣冲嫮顩锋繝濠傚缁诲棙銇勯弽銊у暡闁衡偓閼姐倗纾奸柛灞炬皑瀛濋梺瀹狀潐閸ㄥ綊鍩€椤掑﹦绉甸柛瀣缁傚秴螖閳ь剟鍩為幋锔藉€烽柛娆忣樈濡繝姊洪崨濠冣拹闁搞劌澧庣划瀣吋閸滀胶鍙嗛梺鍓插亞閸犳捇宕㈤幖浣光拺闁告稑锕ゆ慨鍌炴煕閺傝法肖缂侇喖锕崺锟犲磼濠婂拋鍟庨梻浣侯焾缁绘帡宕㈣閹便劑宕奸姀銏紲缂傚倷鐒﹂…鍥虹€电硶鍋撶憴鍕8闁告梹鍨块妴浣割潨閳ь剟骞冮姀銈嗙叆閻庯絽鍚€閻㈠姊婚崒姘偓椋庢濮橆剦鐒界憸宥囧弲闂侀潧鐗嗗ú鐘诲磻閹炬剚娼╂い鎾跺枔閸戔€愁渻閵堝棙绌跨紓宥勭窔閵嗕礁螖閸涱厾锛滃┑鐐村灦椤洭鏁嶈箛娑欌拻濞撴埃鍋撴繛浣冲棗娅i梺璇茬箳閸嬬姵鎱ㄩ妶鍛瀺闁哄啠鍋撶紒缁樼箘閸犲﹥寰勫畝鈧敍鐔兼⒑缁嬫鍎愰柛銊ョ仢閻g兘骞囬弶璺吅闂佹寧娲嶉崑鎾绘煕閵娿儱鈧湱鎹㈠☉姗嗗晠妞ゆ棁宕甸崙褰掓⒑缁嬫鍎滅紒缁樼箞瀵顓兼径濠佺炊闂佸憡娲﹂崜娆忊枍閿濆洨纾藉ù锝呮惈鏍¢梺缁橆殘婵炩偓鐎殿喛顕ч鍏煎緞婵犲嫬骞愬┑鐐舵彧缁蹭粙骞夐垾鏂ユ灁闁哄被鍎查埛鎴犵磼鐎n偄顕滈柟鐧哥秮閺屾盯鎮╁畷鍥р拰閻庢鍠涢褔顢橀崗鐓庣窞閻庯綆浜炲顔尖攽閻橆喖鐏辨繛澶嬬洴椤㈡牠骞囬鈺傜洴閸ㄩ箖骞囨担鐟扮槣闂備線娼ч悧鍡涘疮椤愶箑绀夋慨妯夸含绾捐偐绱撴担鍏夋(妞ゅ繐鐗炵紞鏍叓閸ャ劍鈷掔紒鈾€鍋撴繝娈垮枟閿曗晠宕滃☉銏℃櫖婵犲﹤鍟犻弨鑺ャ亜閺冣偓閺嬬粯绗熷☉銏$厱闊洦妫戦懓璺ㄢ偓瑙勬礃閸ㄥ潡鐛Ο鍏煎珰闁肩⒈鍓﹂崯鍥р攽閻愯埖褰х紒韫矙楠炴顭ㄩ崼鐔告珫濠电偛妫欓幐濠氬煕閹寸姷纾藉ù锝咁潠椤忓牊鍊堕柛妤冨亹閺€鑺ャ亜閺傛寧鎯堥柍褜鍓氱换鍌炴偩閻戣棄绠涢柡澶婃健閺佹粌鈹戞幊閸婃捇鎳楅崼鏇炵煑闁糕剝绋掗埛鎴︽煕濠靛棗顏╅柡鍡樼懇閺屾稒绻濋崟顒€娈岄梺瀹狀嚙缁夌懓顕i幘顔藉亹闁汇垻顣槐鏌ユ⒒娴h櫣甯涢柨姘舵煕閻旈攱鍋ョ€规洘绻堟俊鑸靛緞鐎n剙甯楅梺鑽ゅ枑閻熴儳鈧凹鍓熼幃姗€骞橀鐣屽幍濡炪倖妫侀~澶娾枍婵犲嫧鍋撶憴鍕┛缂佸弶鍎抽銉╁礋椤撴稑浜鹃柨婵嗛娴滄粓鏌嶈閸撶喖藟閹捐埖顫曢柟鎹愵嚙绾惧吋鎱ㄥ鍡楀幋闁稿鎸婚ˇ鐗堟償閵忕媭鈧盯姊洪崫鍕潶闁稿酣浜堕幃鎸庛偅閸愨晝鍘藉┑鈽嗗灣閸庛倝鍩㈤弴銏$厱闁靛牆妫欑粈瀣煛鐏炲墽娲存い銏℃礋閺佹劙宕卞▎妯恍氶梻鍌氬€风粈浣哥暦椤掆偓鐓ら柨鏇炲€哥粻鐐烘煏婵炲灝鍔存繛绗哄姂閺屾盯鍩勯崘鐐暥缂備胶濮靛钘夘潖閾忓湱纾兼俊顖濆亹閻e搫鈹戦悙璺虹毢闁哥姴閰i敐鐐剁疀閹句焦妞介、鏃堝礋椤忓棛鍊為梻鍌欑閹测€趁洪敃鍌氱闁挎洍鍋撻摶鐐烘煥濞戞ê顏痪鎹愭閵嗘帒顫濋浣规倷闂佸搫顑囬崰鏍蓟閻斿吋鍋¢柣妤€鐗婇幃娆忣渻閵堝棙绌跨紒鎻掑⒔閹广垹鈹戦崱鈺傚兊濡炪倖鎸鹃崑妯艰姳婵犳碍鈷掑ù锝勮閻掑墽绱掔紒妯烘诞鐎规洏鍨奸ˇ褰掓煕閳规儳浜炬俊鐐€栫敮鎺楀磹閼姐倖鏆滄繛鎴欏灪閻撴瑥銆掑顒備虎濠碘€炽偢閹藉爼寮介鐔哄帗閻熸粍绮撳畷婊冣枎閹烘柧缃曞┑鐘垫暩閸嬫稑螞濞嗘挸绠板┑鐘宠壘绾惧鏌嶆潪鎵窗婵炴挸顭烽幃妤呮晲鎼存繄鍑归梺鍦缁插潡鎯€椤忓牆绠查柟閭﹀弾濡嫰姊婚崶褜妯€闁哄被鍔岄埞鎴﹀幢濡儤顏¢梻浣筋嚃閸ㄤ即鎮ч幘鎰佸殨濞寸姴顑嗛弲鎼佹煟濡櫣锛嶉柛妯圭矙濮婃椽妫冨☉姘辩暰闂佸搫鎳忛惄顖炲箖濡 鏋庨柟鎯ь嚟閸樻捇鎮峰鍕煉鐎规洘绮岄~婵堟崉閾忚妲舵繝娈垮枟閿曗晠宕滈敃鍌涘€垮ù鐘差儐閻撴稓鈧箍鍎辨鍛婄閻愮數妫柟瑙勫姈椤ュ妫佹径鎰叆婵犻潧妫涙晶鏇灻瑰鍕垫疁闁哄瞼鍠撻埀顒傛暩椤牊绂掑鍫熺厱闁靛闄勯ˉ鍫ユ煛瀹€鈧崰鎾舵閹烘顫呴柣妯虹-娴滃爼姊绘担铏瑰笡闁规悂绠栧畷浼村冀椤撶偠鎽曢梺鎸庣箓椤︻垳鐚惧澶嬬厱閻忕偞宕樻竟妯好归悩鎴愭垹鎹㈠☉姘e亾濞戞瑯鐒介柣顓炴閺屾稑螖娴g硶鏋欓悗娈垮枦椤曆囧煡婢舵劕顫呴柣妯荤垹閸ャ劎鍘卞┑鐘才堥崑鎾剁磼閳ь剚绗熼埀顒€鐣峰鍐殾闁搞儮鏅濋敍婵囩箾鏉堝墽瀵肩紒顔界懇瀹曨偄煤椤忓懐鍘电紓浣割儐椤戞瑩鎮¢崗纰辨闁绘劘灏欑粻鑽も偓瑙勬磸閸旀垿銆佸☉姗嗙叆闁割偅纰嶉弫浠嬫⒒娴g瓔鍤欓柛鎴犳櫕缁辩偤宕卞Ο纰辨锤濠电娀娼ч鎰板极婵犲洦鐓曢柡鍥ュ妼閻忥繝鏌嶉柨瀣瑨闂囧鏌ㄥ┑鍡楊伂妞ゆ帞鍠栭弻锝夊箳濡ゅ啰鏆梺鍝勮閸旀垵顕i弶鎳崇喓鎮伴垾鍏呭濠电娀娼ч鍛存倶閹惰姤鐓ラ柡鍥╁仜閳ь剙缍婂畷鎰節濮橆厾鍙冨┑鈽嗗灟鐠€锕€危鐟欏嫪绻嗙€瑰壊鍠栨晶瀛樻叏婵犲啯銇濋柡灞芥嚇閹瑩鎳犵捄渚純濠电姭鎷冪仦鐣屼桓闂佸搫鏈ú鐔风暦閹偊妲诲銈呮禋閸樹粙銆冮妷鈺傚€烽柡澶嬪灩閻熴劌顪冮妶鍡樺碍闁靛牏顭堥悾鐑藉醇閺囩喎娈濋梺杞扮閺堫剛鍒掗幘鎰佹綎缂備焦蓱婵挳鎮峰▎蹇擃仼濞寸姭鏅犲铏圭矙濞嗗墽鍔搁梺绋匡攻缁诲倿鎮惧畡閭︾叆闁割偆鍠庢禍婊堟⒑缂佹ɑ灏慨姗堢畵楠炴寮撮悙鈺傛杸闂佺粯鍔栧娆撴倶閻斿吋鐓曢柕濠庣厛濞兼劙鏌涙惔顔间喊婵﹦绮粭鐔煎焵椤掆偓椤洩顦归柡浣哥Х缁犳稑鈽夊Ο纰辨О婵$偑鍊曠换鎰偓姘煎墰缁煤椤忓應鎷婚梺绋挎湰閼归箖鍩€椤掑嫷妫戞繛鍡愬灩椤繈顢楁径灞藉Ш闁荤喐绮岀粔鐑芥倶鐎n喗鈷戦柛婵嗗閺嗘瑩鏌涙繝鍌ょ吋闁诡垰鐭傚畷鍗烆渻閺囩偟绉洪柡浣瑰姍瀹曞爼濡搁敂鎯ф锭婵犵數鍋涢悺銊у垝瀹ュ鍋¢柍杞扮贰濞兼牜绱撴担鑲℃垶鍒婇幘顔界厱婵炴垶锕銉╂煛閸℃澧涚紒缁樼洴楠炴鈧潧澹婇弳鈥愁渻閵堝啫濡奸柨鏇樺€濋幃楣冩煥鐎n亶鍤ら梺鍝勵槹閸ㄧ敻宕妸鈺傗拺闂傚牊涓瑰☉姘勃濡わ絽鍟弳鍛節閻㈤潧啸闁轰礁鎲¢幈銊╁箻椤旇姤娅囬梺闈涚墕椤︿即宕戠€n亖鏀介柣妯哄级閹兼劙鏌i幘瀛樼闁哄瞼鍠撻埀顒傛暩椤牆鏆╃紓浣哄亾閸庢娊濡堕幖浣哥畺婵°倕鎳忛弲鏌ュ箹缁厜鍋撳畷鍥跺晥缂傚倷鑳堕搹搴ㄥ储閸忓吋娅犻幖杈剧稻椤洟鏌熼悜姗嗘畷闁稿鍔欓弻褑绠涢敐鍛按婵炲濮伴崹钘夘潖濞差亜浼犻柛鏇ㄥ墯閹疯京绱撴担鍓插剱闁圭懓娲畷娲焵椤掍降浜滈柟鐑樺煀閸旂喓绱掓径灞炬毈闁哄本绋撻埀顒婄秵娴滄粓顢旈鍫熺厵濞撴艾鐏濇俊鍏笺亜閹剧偨鍋㈢€规洖鐖奸弫鎰板川椤掆偓椤ユ岸姊洪懡銈呮瀾闁荤喆鍎抽埀顒佸嚬閸樼偓绔熼弴銏犵濞达絽婀遍崢閬嶆⒑闂堟侗鐒鹃柛鏂跨Ч椤㈡棃鎮╅悽鐢碉紲濡炪倖姊婚埛鍫ュ磿閺冣偓椤ㄣ儵鎮欓弶鎴炶癁閻庢鍣崜鐔风暦椤愶箑绀嬫い蹇撳濡粓姊婚崒娆戝妽閻庣瑳鍛床闁稿本渚楀▓浠嬫煕濞戞﹫鍔熸い鈺傜叀閺岀喖骞嶉纰辨毉闂佺粯鎸婚悷鈺侇潖濞差亜鍨傛い鏇炴噹閸撻亶姊洪棃娑欏缂佽鍟撮獮鍫ュΩ閿斿墽鐦堥梺鍛婂姀閺傚倹绂掗姀鐘斀闁宠棄妫楁禍婊堟煕閻斿憡灏︾€规洘妞介崺鍕礃閳轰緡鈧捇姊虹紒妯虹仸妞ゎ厼瀚伴獮鎺懳旀担鍙夊濠电偠鎻徊浠嬪箟閿熺姴鐤柣鎰劋閻撱儲鎱ㄥΟ鍨厫闁绘挸绻橀弻娑㈩敃閻樿尙鍔撮梺缁樺浮缁犳牠寮婚敐澶嬫櫜闁告侗鍘戒簺闂備礁鐤囬~澶愬垂閸喚鏆﹂柣鎾冲瘨濞尖晜銇勯幋婵堜虎妞ゃ儲宀稿缁樻媴閻熼偊鍤嬬紓浣筋嚙閸婂綊銆冮妷鈺佸窛濠电姴瀚峰ú鎼佹⒑閸濆嫮鈻夐柣蹇斿姍閹兘鏌囬敂鎯у汲闂備礁鎲″ú锕傚储妤e啯鍋傚鑸靛姈閳锋垿鏌涘┑鍡楊仾婵犫偓閻楀牏绠鹃柛娆忣樈閻掍粙鏌熼獮鍨仼闁宠棄顦垫慨鈧柣妯垮皺閳ь剦鍘奸—鍐Χ閸℃ǚ鎷婚梺鍛婎焼閸♀晜姣屽┑鐘垫暩婵兘寮崨濠冨弿妞ゆ挶鍨圭粻顖炴煕閹扮數鍘涢柛姘儔閺屾盯濡烽姀鈩冪彆濠电偛鐗嗛妶绋款潖缂佹ɑ濯撮柛娑橈攻閸庢捇姊哄ú璇插闁靛牏顭堥悾閿嬪閺夋垵鍞ㄥ銈嗘尰婢规洟宕戦幘瀛樺缂侇垱娲橀悗濠氭⒑閸︻厼浜炬繛鍏肩懇閹倿宕熼鍌滅槇闂侀潧楠忕徊鍓ф兜妤e啯鐓ラ柡鍥埀顒佺洴閵嗗倹绂掔€n偀鎷婚梺绋挎湰閻熴劑宕楀畝鈧槐鎺楊敋閸涱厾浠稿Δ鐘靛仦閸旀瑥鐣锋總绋垮嵆闁绘劗顣槐顕€姊绘担鍛婃儓缂佸绶氬畷銏ゅ礂绾拌鲸鏁梻鍌氬€风粈渚€骞夐垾瓒佹椽鏁冮崒姘辩崶濠殿喗顭堥崺鏍磻椤忓牊鐓冪憸婊堝礈閻斿娼栨繛宸簻閹硅埖銇勯幘璺轰粧濠㈣娲栭埞鎴︽倷閹绘帗鍊梺鑽ゅ枂閸庣敻宕洪姀鐙€鍚嬮柛顐亝閳诲本绻濆▓鍨灈闁挎洏鍎遍—鍐寠婢跺本娈鹃梺闈涱煭婵″洨绮婚悙顒佸弿婵妫楅獮鏍煟韫囨挾鎽犳い銊e劦閹瑩骞撻幒鎾搭啋闁诲氦顫夊ú妯兼暜閿熺姴绠栨繛鍡樻尰閸ゆ垶銇勯幒鎴濃偓鐟靶掗崶褉鏀介柣妯垮皺濡嫰鏌℃径濠勬皑闁稿鎹囧鎾閻樼數鏋冮梺纭呭閹活亞寰婇崸妤佸剹闁糕剝绋掗悡鏇㈡倶閻愭潙鍔ら柛銈庡墴閺岋綁寮幐搴&闂佽鍠栫紞濠囧箹瑜版帗鍋¢柟娈垮枟椤撶粯绻濆▓鍨灈闁挎洏鍎甸妴鍐川缁厜鍋撻敂鐐磯闁靛绠戦弸鍌炴⒑閸涘﹥澶勯柛鎾寸洴钘濋柡澶婄氨閺€鑺ャ亜閺冨倶鈧螞濮橆厾绠鹃柛婊冨暟缁夘喗顨ラ悙鑼闁诡喒鏅濋幏鐘绘嚑椤掑鏂€闂傚倷绀佸﹢閬嶅磿閵堝鍨傞柛顐f礃閸庡﹪鏌ㄥ┑鍡樺窛缁惧彞绮欓弻娑氫沪閹规劕顥濋梺閫炲苯澧柟鑺ョ矌閸掓帡寮崼婵堥獓闂佺懓鐤囧▍鏇犵矙閹达箑鐓橀柟杈剧畱楠炪垺绻涢崱妯哄妞ゆ梹娲樼换婵嬫偨闂堟刀銏ゆ煥閺囨ê鈧繂鐣烽鐐村亹闁告瑥鍋婄紞浣哥暦婵傜唯闁挎梹鍎崇敮楣冩⒒婵犲骸浜滄繛灞傚€涙晶婵嬫⒑缁嬫鍎愰柟鐟版搐閻e嘲顫滈埀顒勭嵁閹捐绠抽柛鈩兠惁鏌ユ⒒閸屾艾鈧悂宕愰幖浣哥9濡炲娴烽惌鍡椕归敐鍛础闁绘繆娉涢埞鎴︽偐閸欏鎮欑紒鐐礃椤曆囧Υ閹烘埈娼╅柨婵嗘噸婢规洟鏌f惔銈庢綈婵炲弶锚鐓ら柣鏂款殠閸ゆ洖鈹戦悩瀹犲閸烆垶姊洪棃娑崇础鐎广儱娲g憰鍡涙⒒閸屾艾鈧兘鎮為敃鍌涘剳鐟滅増甯掗崹鍌滄喐閻楀牆绗掔紒鐘靛枛閺屻劑鎮㈤崫鍕戙垻鐥幆褜鐓奸柡灞界Ч閸┾剝鎷呴崨濠冾啀缂傚倷鑳舵繛鈧紒鐘崇墵瀵鈽夐姀鐘靛姶闂佸憡鍔楅崑鎾绘偩閼测晝纾藉ù锝呮惈鍟告繝鈷€鍕垫疁濠碉紕鏁诲畷鐔碱敊閸撗勬緫闂備焦瀵х换鍌溾偓姘煎櫍瀵偊寮介銈囷紳婵炶揪绲肩划娆撳传濞差亝鍋ㄦい鏍ュ€楃弧鈧悗瑙勬礃濡炰粙宕洪埀顒併亜閹哄秹妾峰ù婊勭矒閺岀喖鎮滃Ο铏逛淮濡炪倕绻嗛弲鐘诲蓟閿濆绠抽柟瀵稿С缁敻姊洪棃娑欐悙閻庢矮鍗抽悰顕€骞掑Δ鈧粻锝嗙節閸偄濮冮柣銉邯濮婄粯鎷呴悷鎵虫灆闂佽 鍋撻梺顒€绉撮崹鍌炴煕椤垵娅樻繛鍏肩墪閳规垿鎮╃€圭姴顥濋梻浣稿船濞差參寮婚敐澶婄睄闁逞屽墯缁傚秵绂掔€n亞鍔﹀銈嗗笂缁€浣虹箔閹烘挶浜滄い鎾偓鍐插Х濡炪倧闄勬繛濠囧蓟閿濆鐓涘┑鐘插€绘禒鎼佹倵濞堝灝鏋涙い顓犲厴楠炲啴濮€閵忕姵鐎抽柡澶婄墑閸斿秴鈻嶉幘缁樷拻濞达綀娅g敮娑㈡煙缁嬫寧鎲搁柤娲憾瀹曞ジ寮撮悙纰夌幢闂備浇顫夊畷姗€顢氳缁粯瀵奸弶鎴狀啇闁诲孩绋掗…鍥╃不濡偐纾奸柣妯哄暱閸濇椽鏌″畝瀣ɑ闁诡垱妫冩慨鈧柍鍨涙櫅椤本淇婇悙顏勨偓銈夊储閻撳篃娲敇閵忕姷鐣洪梺姹囧€ら崹顒佺瑜版帗鐓欓柣鎴炆戠亸鐢告煕濡粯宕岄柟顔煎槻椤劑宕熼鐘靛帨闁诲氦顫夊ú妯煎垝瀹€鍕厺閹兼番鍔岀粻濂告煕閹般劍娅嗘繛鍛濮婄粯鎷呴悷閭﹀殝缂備浇顕ч崐鑳濡炪倖鐗楃划搴㈢▔瀹ュ洨纾藉ù锝夘€囧鍕洸婵犲﹤鐗婇悡娑㈡煕閹扳晛濡奸柍褜鍓涢弫濠氱嵁韫囨稑鐒洪柛鎰典簽椤旀洟姊虹紒妯诲碍闁告垳绮欓悡顒勵敆娴g懓寮挎繝鐢靛Т閹冲繘顢旈悩鐢电<閺夊牄鍔岀粭鎺楁懚閿濆鐓曢煫鍥ㄦ礀鐢爼鏌$€e墎鐣垫慨濠勭帛閹峰懏绗熼婊冨Ъ婵$偑鍊栭崹闈浳涘┑瀣祦闁规壆澧楅崵鎺楁煏閸繃顥滈幖鏉戯工閳规垿鎮欓弶鎴犱户闂佹悶鍔嶅钘夌暦閹达箑纾奸柣鎰皺椤旀劙姊洪崷顓涙嫛闁告ê銈搁幃姗€濡烽埡鍌滃幈濠殿喗顭囬崢褎绂嶅鍫熺厓閻熸瑥瀚悘瀛樸亜閵忥紕鎳呮繛鎴犳暬閹粓鎮剧仦钘夊唨婵犵數濮烽弫鎼佸磻濞戙垹绠柟瀵稿Т缁躲倝鏌涢…鎴濇殠闁挎繂顦粻娑㈡煛婢跺孩纭舵い鏂匡躬濮婃椽鎮烽弶鎸庢瘣缂佸墽铏庨崣鍐ㄧ暦娴兼潙鍐€鐟滃繘寮抽敂鎴掔箚闁靛牆鎳忛崳娲煕鐎n亜鈧潡鐛弽顬ュ酣顢楅埀顒勬倶椤旀祹褰掓偐閼碱剛鍔┑顔硷工椤嘲鐣烽幒鎴僵妞ゆ垼妫勬禍楣冩煟閹达絽袚闁搞倕瀚伴弻娑㈩敃閿濆棛锛曢梺閫炲苯澧剧紒鐘虫尭閻i攱绺界粙璇俱劍銇勯弮鍥撴繛鍛墦濮婄粯鎷呴搹骞库偓濠囨煕閹惧绠樼紒顔界懇楠炲鎮╅崗鍝ョ憹濠电偛顕崢褔鎮洪妸鈺傚亗闁绘ɑ绁撮弨鑺ャ亜閺冨洦顥夊┑顔兼喘閺屽秷顧侀柛鎾村哺閹囧即閵忊€充患闂佺粯鍨煎Λ鍕儗濡も偓椤法鎹勯搹鍦紘濡炪倖姊瑰ú鐔奉潖濞差亝鍋¢柟娈垮枟閹插ジ姊洪懡銈呮瀭闁稿海鏁婚獮鍐潨閳ь剟銆侀弮鍫濋唶闁绘柨鎼獮鍫ユ⒑鐠囨彃鍤辩紓宥呮缁傚秴顭ㄩ崼婵堝姦濡炪倖宸婚崑鎾寸箾绾绡€闁诡喕鍗抽、姘跺焵椤掆偓椤曪絾绂掔€e灚鏅濋梺闈涚箳婵攱绂嶆导瀛樷拺闁煎鍊曢弸鎴︽煟閻旀潙鍔ら柍褜鍓氬銊╁礂濮椻偓瀹曟椽鍩€椤掍降浜滈柟鍝勬娴滄儳鈹戦埥鍡椾簼缂佽鐗嗛锝嗙節濮橆厼浜滈梺鎯х箰濠€閬嶆偂閹剧粯鈷戦柛鎾瑰皺閸樻盯鏌涢悩鎰佹當闁崇粯鎹囧畷婊勬媴閾忕櫢绱冲┑鐐舵彧缁茶偐鍒掑▎鎾充紶婵炲樊浜濋悡娆戠磼鐎n偒鍎ラ柣鎾冲悑椤ㄣ儵鎮欓懠顒傤啋閻庤娲忛崝鎴︺€佸▎鎴犵<闁靛骏绱曢妶顐︽⒒娴g瓔鍤欓柛鎴犳櫕缁辩偤宕卞Ο纰辨锤濠电娀娼ч鍛不閻樺磭绠鹃柛鈩兩戠亸浼存煃闁垮绗掗棁澶愭煥濠靛棙鍣洪柛鐔哄仱閹綊骞囬崜浣虹槇闂佸搫鐬奸崰鏍箹瑜版帩鏁冮柨婵嗘噽椤f煡姊虹紒妯诲蔼闁稿﹥绻堝濠氬即閵忕娀鍞跺┑鐘茬仛閸旀牗鏅ラ梻鍌欒兌椤牓顢栭崒鐐茬柧闁绘顕ч拑鐔兼煥濠靛棭妲哥紒鐙呯秮閺屻劌鈹戦崱姗堢礊濠碘槅鍋勭€氼喚妲愰幘瀛樺闁告繂瀚呴敐鍛斀闁绘劘顕滈煬顒傗偓娈垮枛椤兘骞冮姀銏″仒闁炽儱鍘栨竟鏇炩攽閻愭潙鐏︽い蹇庡嵆楠炲鏁冮埀顒勬偂閺囥垺鐓欓柟娈垮枛椤eジ鏌i幘璺烘灈妤犵偞鐗滈崚鎺旀喆閸曞灚缍夐梻浣虹帛閹告悂宕ョ€n喖绠為柕濠忓缁♀偓闂佸憡渚楅崳顔界閳轰讲鏀介柣鎰綑閻忊晠鏌℃担绛嬪殭闁伙絿鍏樻俊鎼佸煛婵犲啯娅撻梻浣侯焾缁绘劙濡堕幖浣告瀬妞ゅ繐妫涚壕浠嬫煕鐏炴崘澹橀柍褜鍓涢崗姗€骞冮悙鐑樻櫇濞达絽鍚€濮规姊洪崨濠傚Е闁绘挸鐗撻幃鐐寸鐎n偆鍙嗛梺缁樻煥閹碱偄鐡紓鍌欒兌婵敻鎮ч弴銏$畳闂備胶顭堢换鎰板触鐎n剛绀婇柟杈剧畱閼歌銇勯弽顐沪闁抽攱鍨块弻娑㈠箛椤掆偓缁狙囨煙椤栨氨澧﹂柡灞剧⊕缁绘繈宕熼浣圭槗婵°倗濮烽崑娑氭崲閹烘梹顫曢柟鐑樺殾閻斿吋鍤冮柍鍝勶工閺咁參姊绘担鍛婃儓妞わ富鍨堕幃褔宕卞Ο缁樼彿婵炲濮撮鍛矆閸℃褰掓偂鎼达絾鎲奸梺缁樻尰閻熲晠骞冭ぐ鎺戠倞闁搞儜鍕闂佷紮绠戦悧鍡氱亙闂佺粯锕㈠褎绂掑鍕╀簻闁挎洑妞掗崥顐︽煕閹烘挸绗掗柍璇查叄楠炲洭顢橀悙鎻捨ら梻鍌欐祰椤宕曢幎鑺ュ仱闁靛ň鏅涚痪褔鏌涘☉姗堟缂佽妫濋弻锝夊箛閸忓摜鐩庨梺閫炲苯澧柣妤佹礋閿濈偠绠涢弮鍌滅槇濠殿喗锕╅崜娑㈡晬濞戙垺鈷戦悷娆忓缁€鍐┿亜閺囧棗鍞瀹曪絾寰勯崼婊呯泿闂備礁婀遍崕銈夊垂閻㈠壊鏁傛い蹇撶墛閻撶喖鏌熼幆褏锛嶇紒鐘差煼閺岋紕浠﹂崜褎鍒涢梺绯曟櫅鐎氭澘鐣峰鈧幃娆擃敆閸屾稒顔旈梻鍌氬€风粈渚€骞栭鈶芥稑鈽夐姀鐘碉紱闂佺粯姊婚崕銈夛綖閺囥垺鐓欓柣鎴炆戦埛鎺旂棯閹冩倯濞e洤锕、娑樷攽閸℃洘鐫忛梻浣圭湽閸婃洜鈧矮鍗抽獮鍐ㄎ旈崘鈺佹瀭闂佸憡娲﹂崜娑⑺囬妸鈺傗拺缂佸娼¢妤呮煏閸喓鎽冩俊顐ゅ枛濮婃椽宕烽鈩冾€楅梺鍝ュУ椤ㄥ﹪骞冮敓鐘冲亜闁稿繗鍋愰崣鍡椻攽閻樼粯娑ф俊顐g懇钘熼柣鎰劋閻撳繘鏌涢妷锝呭缂佺姵鐗犻弻鐔哥瑹閸喖顬夌紓浣虹帛缁诲牆鐣烽妸鈺婃晪闁告侗鍓欓幗瀣磽閸屾艾鈧嘲霉閸ャ劊浠堥柛婵勫劜閺嗘粓鏌熼悜妯荤濞存粈绮欏缁樻媴閻熸澘濮㈢紓浣虹帛閿曘垽宕洪埀顒併亜閹哄秷鍏岄柕鍡樺笧缁辨帡鍩€椤掑嫬绀冮柕濞垮灪閺傗偓闂備胶绮摫妞ゆ梹鐗犲鎶筋敍濞戞绠氶梺鍦帛鐢宕甸崶鈹惧亾鐟欏嫭绀冮柛銊ョ仢閻g兘鎮㈢喊杈ㄦ櫍濠电偞鍨剁湁濠㈣娲栭埞鎴︻敊閺傘倓绶甸梺绋款儏鐎氼剟鎮鹃悽绋垮耿婵妫欓鏃堟⒑缂佹ê濮堢憸鏉垮暣瀵娊鏁愭径瀣幈闂侀潧艌閺呮繈鎮鹃搹鍏夊亾濞堝灝娅橀柛鎾跺枑娣囧﹪鎮滈懞銉︽珕缂傚倷鐒﹂…鍥╃矓妤e啯鈷掗柛灞捐壘閳ь剟顥撳▎銏狀潩椤掑鍔烽悷婊冮叄閵嗗啴濡烽妸褏鏉搁梺鍝勬川閸c儱顭囬悢鍏尖拺闁告繂瀚崒銊╂煕閵娿儳绉虹€规洘甯℃俊鎼佸煛閸屾粌骞堟繝寰锋澘鈧洟宕锝囶洸鐟滅増甯楅悡娑㈡煃瑜滈崜姘辩矉閹烘柡鍋撻敐搴′簽闁告ü绮欏楦裤亹閹烘垳鍠婇梺鍛婎焽閺咁偆妲愰悙鍝勭闁挎梻鏅崢浠嬫椤愩垺鎼愭い鎴濇嚇瀹曟繈濡舵径瀣帗閻熸粍绮撳畷婊冣攽鐎e墎绋忔繝銏f硾閳洖煤椤忓懏娅囬梺绋挎湰濮樸劑藝椤撱垺鈷戠紓浣股戦埛鎺楁煕濡姴鎳愭稉宥夋煛瀹ュ啫濡介柛娆忕箲娣囧﹪鎮欐0婵嗘婵炲瓨绮撶粻鏍ь潖閾忚瀚氶柍銉ㄦ珪閻忊偓闂備礁鎼幊鎰箾閳ь剚顨ラ悙鎻掓殲缂佸倹甯為埀顒婄秵閸嬪嫭绂掗搹鍦<闁绘劦鍓氱欢鍙夈亜閿曚線鍝洪柟顖涙⒐缁绘繈宕橀鍡欐闂備焦鐪归崹钘夘焽瑜庣粋鎺楁晝閸屾稓鍘电紓浣割儐椤戞瑩鎮℃總鍛婄厵闁惧浚鍋嗙粻鏍煏閸剛绉€规洘锕㈤崺锟犲磼濞戞艾绲块梻鍌氬€烽悞锔锯偓绗涘厾娲冀椤撶偟锛欓悷婊呭鐢帞澹曟繝姘厓闁告繂瀚崳娲煟閹捐泛鏋涢柡灞炬礉缁犳盯寮撮悙鎰剁秮閺屾盯鎮㈤崫鍕闂佸搫鐭夌紞渚€鐛Ο灏栧亾閸偅鍋犻柍褜鍓氱敮锟犲蓟瀹ュ牜妾ㄩ梺鍛婃尰閻熲晛鐣烽姀鐙€鐓ラ柛顐g箘閿涙盯姊洪悷鏉库挃缂侇噮鍨跺畷鎰版偨閸涘﹦鍙嗗┑鐘绘涧濡繈顢撳Δ鈧…鑳槺闁告濞婇獮蹇涘箣閿旂晫鍔堕悗骞垮劚濡矂骞忕紒妯肩閺夊牆澧介幃濂告煟閳╁啯顥堢€规洜鏁诲畷姗€顢欓悾灞藉箞闂備線娼ч…鍫ュ磿闁秵鍤嬬憸鐗堝笚閹虫岸鏌i幇顔煎妺闁绘挻娲熼弻鐔稿鐎涙ɑ閿梺鍝勵儐濡啴寮诲鍫闂佺绻戠粙鎾跺垝閸喓鐟归柍褜鍓熷畷娲Ψ閿曗偓缁剁偛鈹戦悩鎻掝劉鐎点倖妞藉铏瑰寲閺囩偛鈷夐梺鑽ゅ枂閸庨亶顢氶敐澶婄闁兼亽鍎幏缁樼箾鏉堝墽鍒伴柟璇х節瀹曨垶鎮欓悽鐢碉紲闁诲函缍嗛崑鍕倶鐎涙﹩娈介柣鎰皺缁犵粯顨ラ悙宸剶闁诡喒鏅犻幃钘夆枔閹稿巩锔界節閻㈤潧浠╅柟娲讳簽瀵板﹪鎳為妷褏褰炬繝鐢靛Т閸嬪棝鎮炴禒瀣厸鐎广儱鍟俊璺ㄧ磼閻樻彃鈷旈柍褜鍓涢幊鎾寸珶婵犲洤绐楅柡鍥╁Ь婵娊鎮归崶顏嶆⒖鐟滅増甯楅崵鍐煃鏉炴媽顔夐柡瀣嚇濮婃椽宕崟顒佹嫳濠电偛寮堕敋妞ゆ洏鍎靛畷鐔碱敍濮樿泛鏁规繝鐢靛█濞佳兾涘Δ鍚藉鈹戠€n偀鎷绘繛杈剧悼閹虫捇顢氬鍛<閻犲洦褰冮埀顒佺摃閻忓鏌熼崗鑲╂殬闁搞劌顭烽妴鍛村矗婢跺瞼鐦堟繝鐢靛Т閸婄粯鏅跺☉銏$厽闁规儳纾粻浼存煃鐟欏嫬鐏撮柟顔界懇閹崇娀顢栭懗顖涱€楅梻鍌欑閹测€愁潖婵犳艾鏋侀柟闂寸閻掑灚銇勯幒鎴濇灓婵炲吋鍔欓弻鐔碱敊閼测晛鐓熼悗瑙勬礃濞茬喎顕f繝姘ㄩ柕澶婂嚱缁犳捇寮诲☉銏犲嵆闁靛鍎虫禒鈺呮⒑閸涘娈欐繛鍛礋婵$敻宕熼鍓ф澑闂佸湱鍋撻幆灞轿涢妶澶嬪仩婵﹢绠栧顔记庨崶褝韬┑鈥崇埣瀹曞爼鈥栭鍝勫姦闁哄本绋撻埀顒婄秵閸撴瑦绂掓潏顭戞闁绘劖娼欓悘瀵糕偓瑙勬礀閻栧ジ銆佸Δ鍛<婵ü绌堕崑濠囨⒒閸屾瑧顦︽繝鈧柆宥呯?闁靛牆顦崹鍌炴煟閺冨倸甯剁紓浣叉櫅闇夐柣妯烘▕閸庢劙鏌i幘瀛樼闁靛洤瀚伴獮鍥礈娴g懓浠圭紓鍌欒兌婵敻骞愭繝姘疄闁靛ě鍕瀭闂佸憡娲﹂崢鐓庮嚕閵娿儮鏀芥い鏃傘€嬪銉︺亜椤撶偛妲婚柣锝囧厴楠炴帡骞嬮弮鈧悗濠氭⒑鐟欏嫭鍎楅柛妯衡偓鐔插徍闂傚倸鍊搁崐宄懊归崶顒婄稏濠㈣泛鐬奸惌鍫ユ煙缂併垹鏋涚紒鈧崼鐔虹瘈闂傚牊绋撴晶銏㈢磼閻樿櫕顥堥柡宀嬬秮瀵噣宕惰濡叉劙姊洪崫鍕殭闁绘妫楅蹇撯攽閸ャ儰绨婚梺瑙勫礃濞夋稒绂掕閺屽秷顧侀柛鎿勭畵瀹曪綁宕橀…鎴炵稁闂佹儳绻楅~澶愬窗閸℃稒鐓曢柡鍥ュ妼娴滄粌鈹戦鍏煎暈缂佺粯绻傞埢鎾诲垂椤旂晫浜栭梻浣侯焾閿曘儳鎹㈤崒鐑嗘晪闁挎繂顦拑鐔兼煏婢舵ê鏋熼柡鍛灪缁绘稒娼忛崜褏袣濠电偛鎷戠紞渚€骞嗘笟鈧畷濂稿Ψ閿旇瀚介梻浣侯焾閺堫剙顫濋妸锔芥珷婵炴垶姘ㄧ壕濂告倵閿濆骸浜滅紒妤佸笚閵囧嫰寮捄銊ь唶闂佸疇顫夐崹鍨暦婵傜顫呮い顐枤鎼村﹪姊婚崒娆掑厡缂侇噮鍨堕垾锕傚醇濠靛牊娈鹃梺姹囧灩閹诧繝宕戦埡鍛叄闊洦鎸哥敮銊╂煕鐎n偅灏柍缁樻崌瀹曞綊顢欓悾灞奸偗闂傚倷鑳剁划顖炴偋濠婂牆鍌ㄧ憸鏃堝箖妤e啯鍊婚柤鎭掑劚娴滄鏌熼悡搴f憼閽冮亶鏌¢崒妤€浜鹃梻鍌氬€烽懗鍓佹兜閸洖鐒垫い鎺嗗亾缁剧虎鍘剧划濠氬蓟閵夛箑鈧敻鏌涢…鎴濅簽濠⒀嗕含缁辨帗娼忛妸锕€纾抽悗瑙勬礃鐢帡鍩㈡惔銊ョ妞ゆ挾鍟樺鍕箚闁绘劦浜滈埀顑懐纾芥慨妯哄船閸ㄦ繃绻涢崱妤冪闁哄棴闄勭换婵囩節閸屾粌顤€闂佺顑呯€氫即寮婚敐澶婄闁惧浚鍋勯弨顓㈡⒑绾懎袚婵炲弶鐗犻崺鐐哄箣閿旇棄鈧兘鏌℃径瀣仼濞寸姵鎮傚铏瑰寲閺囩喐鐝旈梺鍝ュ枑濞兼瑩鎮鹃悜钘夌闁挎洍鍋撶紒鐘哄吹缁辨挻鎷呴懖鈩冨灥閳诲秴顭ㄩ崼鐔哄幍闂佺粯鎸稿ù鐑藉箺閻樼數纾奸悹鍥ㄥ絻椤忣參鏌熼姘仾闁诡垱妫冩俊鎼佹晜鐟欏嫬顏归梻鍌氬€风欢锟犲磻閸℃稑纾绘繛鎴欏灪閸ゆ劖銇勯弽銊р姇婵炲懐濮甸妵鍕籍閸屾稒鐝紓浣哄Т婢т粙鎯€椤忓牜鏁囬柕蹇婃櫆椤ユ牜绱撴担鍙夘€嗛柛瀣崌濮婄粯鎷呯粵瀣異闂佸摜濮靛ú鐔风暦閿熺姴绠┑顔藉姀閸嬫挻鎷呯化鏇熺€婚梺瑙勫劤椤曨參宕i崱妤婃富闁靛牆妫涙晶顒勬煟椤撗冩灍缂佹梻鍠栧鎾閳锯偓閹锋椽姊洪崷顓х劸婵炴挳顥撶划濠氬箻閸撲胶锛滈梺闈涱焾閸斿本绂嶈ぐ鎺撶厾婵炲樊浜欓幉鐐殽閻愯揪鑰挎い銏$懇閹墽浠﹂挊澶岊唶闂傚倸鍊风欢姘跺焵椤掑倸浠滈柤娲诲灡閺呭爼顢涘鍛紲闂佺鏈粙鎴犵箔瑜旈弻宥堫檨闁告挶鍔庣槐鐐哄幢濞戞锛涢梺绯曞墲缁嬫垿宕掗妸鈺傗拺妞ゆ巻鍋撶紒澶屾暬閸╂盯骞嬮悩鍨紡濡炪倖鎸鹃崑鐐哄闯瑜版帗鐓熼柟鍝勭Ф閻瑩鏌$仦鍓ф创鐎殿噮鍓涢幑鍕Ω閹扳晛鐏查柡灞界Ф閹风娀鎳犻顐庡應鍋撶憴鍕闁绘牕銈搁妴浣肝旀担鐟邦€撻梺鍛婄箓鐎氼剛绮鑸碘拺闁煎鍊曢弸鎴犵磼椤旇偐肖闁告帗甯¢獮妯虹暦閸ャ劍顔曟繝鐢靛Т閿曘倝宕板顒夌劷闁冲搫鍊舵禍婊堟煙閻戞ê鐒炬俊鎻掔秺閹妫冨☉姘卞姱濠殿喖锕ュ浠嬪箠閻愬搫唯闁告劕褰為柇顖炴寠濠靛鐓㈡俊顖欒濡牓鏌i幒宥囩煓闁哄备鈧剚鍚嬮幖绮光偓宕囶啈闂備胶绮幖顐ょ礊娓氣偓閹繝顢曢敃鈧悙濠囨煏婵犲繐顩い锔哄姂濮婃椽骞栭悙娴嬪亾閹版澘纾婚柟鍓х帛閳锋垿鎮归崶銊у弨妞ゅ孩顨婇弻锝堢疀閺傚灝鎽甸梺璇″櫙缁绘繈寮幘缁樺亹闁艰壈鍩栭幉浼存⒒娴h姤纭堕柛鐘虫尰閹便劑骞橀钘夆偓宄扳攽閻樺弶澶勯柣鎾冲暣瀵爼鎮欓棃娑辨毉濡炪倧绠撻ˉ鎾舵閹烘鏁婇柤娴嬫櫅閻撶喎鈹戦纭锋敾婵$偠妫勯悾宄邦潨閳ь剟鐛幘璇茬闁圭偓鏌¢弲娑⑩€旈崘顔嘉ч煫鍥ㄦ礈閺嗐垺绻涚€涙鐭ら柛鎾寸懃瀹撳嫰姊洪崷顓烆暭婵犮垺顭囩划缁樼節濮橆厼鈧灚绻涢幋鐑嗕痪妞ゅ繐鐗滈弫渚€鏌熼崜褏甯涢柍閿嬪灴閺屾稑鈽夊鍫熸暰闁诲繐绻戞竟鍡涘箟閹间礁绾ч柛顭戝枟濞堝鎮楃憴鍕缂侇喗鎹囧濠氬幢濡ゅ﹤鎮戦梺绯曞墲閻熴儵鐛Δ鍛拻濞撴埃鍋撴繛浣冲懏宕查柛鈩冪☉閻ょ偓绻涢幋娆忕仾闁稿﹤鐖奸弻銈囧枈閸楃偛顫紒鐐礃閸嬫劗妲愰幘瀛樺閻犲浄绱曢崝椋庣磽娴e搫校闁圭懓娲濠氭晲婢跺娅滈梺鎼炲劀閸愩劎顓洪梺璇叉唉椤煤閿曞倸纾诲┑鐘插€婚弳锕傛煟閺冨倸甯堕幆鐔兼⒑閹稿孩鈷掔紒顕呭灣缁辩偛鐣濋崟顑芥嫽闂佺鏈悷褏绮i弮鈧换娑欐媴閸愬弶鍣虹€规洘鐓¢弻鐔兼倻濡闉嶉梺鍛婄懃缁绘﹢寮婚敐澶婄闁绘ê鐏氶幉姗€姊烘潪鎵槮闁挎洏鍊濋崺鐐哄箣閿旇棄浜归梺鍛婄懃椤︻垶藝閳哄懏鈷戦柟鎯板Г閺侀亶鏌涢妸銉﹀仴鐎殿喛顕ч埥澶愬閳╁啯鐝曢梺鑽ゅТ濞诧箒銇愰崘顏嗕笉閻熸瑥瀚粻楣冩倵閻㈡鐒鹃弽鈥斥攽閿涘嫬浠掔紒顔界懃椤曪絿鎷犲ù瀣潔闂侀潧绻掓慨鐢杆夊┑瀣厽闁绘ê鍘栭懜顏堟煕閺傚灝顒㈤悗闈涖偢瀹曞爼鍩¢崘顏庣闯濠电偠鎻徊楣冨垂濠靛瑙︽い鎰堕檮閻撴洟鎮楅敐搴″濞寸姍鍥ㄧ厵妤犵偛鐏濋悘鈺呮煃鐟欏嫬鐏╅柍褜鍓ㄧ紞鍡樼閻愬搫纾归柣鎰劋閸嬧剝绻濇繝鍌氭殻闁告瑥瀚伴弻鐔碱敊缁涘鐤佸銈冨灪椤ㄥ﹤鐣烽悢纰辨晞闁兼亽鍎遍褰掓⒒閸屾瑧绐旀繛鑹板吹閳ь剟娼ч惌鍌氱暦閵忥紕闄勯柟鑲╁亹閸嬫捇宕掗悙鑼槯闂佸吋绁撮弲婵嬫儊閸儲鈷戦梻鍫熺〒缁犳碍淇婇幓鎺戭伃闁硅櫕鎹囧畷绋课旀担鍝勫箰闂佽绻掗崑鐔兼偤閺冨牆纾块柡鍐ㄥ€甸崑鎾舵喆閸曨剛顦ラ梺缁樼墪閸氬绌辨繝鍌ゆ桨鐎光偓婵犲唭顒勬⒒娴i涓茬紒鐘冲灴閹囧箻閹颁焦缍庡┑鐐叉▕娴滄繈藟閸喓绠鹃柟瀵稿仦閻ㄦ垿鏌i敐澶岀暫婵﹥妞藉畷顐﹀礋椤掆偓濞呫倗绱撴担鍓插剱閻㈩垪鈧剚鍤曢柡灞诲劚闁卞洭鏌¢崶銉ュ闁哄拋鍓熷铏圭磼濡搫顫屽銈嗘处閸欏啫鐣烽姀銈嗗仺闁告稑艌閹锋椽鎮峰鍛暭閻㈩垱顨婇弫宥夋偄閸忚偐鍘鹃梺鍛婂姌鐏忔瑩宕洪敐澶嬬厵妞ゆ棁妫勯崝銈夋偂閵堝棎浜滈煫鍥ㄦ尰閸d粙鏌涘鈧褔鈥旈崘顔嘉ч柛鈩冪懃椤冾渻閵堝啫濡奸柟鍐茬箳缁顓兼径瀣偓閿嬨亜閹达絾纭剁紒鐘冲哺濮婅櫣绱掑Ο鍝勑曟繛瀛樼矋缁捇宕洪埀顒併亜閹哄秶鍔嶇紒鈧崼銉︾厵妤犵偛鐏濋悘鍙夘殽閻愬弶鍠橀柟顔ㄥ洤閱囨繝闈涙噽缂嶅秴鈹戦悩鍨毄濠殿喗鎸抽弫鍐Χ婢跺浜遍梺绯曞墲缁嬫垿宕欓悩灞傗偓鎺戭潩閿濆懍澹曢梻浣告惈閺堫剟鎯勯娑楃箚闁绘垹鐡旈弫濠囨煟閹惧啿鐦ㄦ繛闂寸矙濮婄粯鎷呴搹鐟扮闂佽鎮傜粻鏍х暦娴兼潙鍐€妞ゆ挾鍋犻幗鏇㈡⒑缂佹ɑ鈷掗柛妯犲懐涓嶉柕澶涜礋娴滄粓鏌¢崘銊モ偓鐢稿箯閿熺姵鐓涢柛鈾€鏅涢獮鏍煃鐟欏嫬鐏撮柟顔界懇瀵爼骞嬮悙鍨潥闂傚倷鐒﹂幃鍫曞磿椤栫偛绀夐幖娣妼閸屻劌霉閻樺樊鍎愰柍閿嬪灴閹嘲鈻庤箛鎿冧患缂備讲鍋撻柛鎰ㄦ櫇缁犳儳顭跨捄渚剳婵炴彃顕埀顒侇問閸犳岸鈥﹂崼銉ョ叀濠㈣泛艌閺嬪酣鏌熼柇锕€澧ù鐓庨閳规垿鎮╅崹顐f瘎婵犳鍠楅幐鍐茬暦椤栫儐鏁嶉柣鎰棘閿旂晫绡€闂傚牊绋撴晶鎰版煕鐎n偅灏甸柟鍙夋尦瀹曠喖顢楅埀顒勊囬埡鍛拺缂佸顑欓崕蹇涙煥閺囨ê鈧繈骞冩ィ鍐╁€婚柤鎭掑劚娴滄粎绱掗悙顒€顎滃瀛樻倐瀵煡濮€閿涘嫮顔曢柡澶婄墕婢т粙骞冩總鍛婄厵闁惧浚鍋呭畷灞俱亜閵忊剝鈷愰悗浣冨亹閳ь剚绋掕彜闁瑰嘲顭峰铏圭矙閹稿孩鎷遍梺鑽ゅ枂閸旀垵鐣峰Δ鈧悾婵嬪礋椤掑倸骞堥梺纭呭閹活亞寰婃ィ鍐ㄦ辈妞ゆ帒鍊甸崑鎾斥枔閸喗鐏嶉梺缁樻惈缁绘繂鐣峰ú顏呮櫢闁绘ɑ褰冪粣娑橆渻閵堝棙灏甸柛瀣枛閸┾偓妞ゆ帒顦顕€鏌″畝瀣М闁诡喒鏅犻幃婊兾熺化鏇炰壕闁告劦鍠楅崑锝夋煃瑜滈崜鐔煎极閸愵喖纾兼慨姗嗗墯閸庮亪姊绘担鍛婃儓婵炲眰鍔戝畷浼村幢濡⒈娲稿┑鐘诧工閻楀﹪鎮″▎鎾寸厸濠㈣泛锕︽禒銏°亜閿濆棗鈻曢柡宀嬬秮閺佹劙宕煎鍐╁創缂傚倷娴囨ご鍝ユ暜閿熺姴绠栭柍杞拌兌閺嗭箓鏌涢妷顖滃埌妞ゎ偄鐭傚缁樼瑹閳ь剙顭囪鐓ら柕鍫濇礌閸嬫挸顫濋鐔哄嚒濡炪倖娲╃徊鍓х矉閹烘柡鍋撻敐搴樺亾椤撴稒娅囬柟鍙夌摃缁犳稑鈽夊▎蹇庣暗闂備胶顭堥惉濂稿磻閻愬搫鐓曢柟杈鹃檮閻撴洘绻濋棃娑欘棞妞ゅ繐鐡ㄦ穱濠囧箵閹烘梻楔闂佸搫鐬奸崰鏍€佸▎鎾村亗閹煎瓨锚娴滈箖鏌熼梻瀵哥瓘缂傚秵鐗犻悡顐﹀炊閵婏箑顎涘┑鐐叉▕娴滃爼寮崒鐐寸厱闁哄洢鍔嬬花浠嬫煟閹邦剨韬慨濠勭帛閹峰懘宕ㄦ繝鍌涙畼婵犵數鍋犻婊呯不閹惧磭鏆︽繝濠傚暊閺嬪酣鏌熺€电啸妤犵偞鎸搁埞鎴︽倷閺夋垹浠搁梺鑽ゅ暀閸涱厼袣闂侀€炲苯澧柍瑙勫灴閹瑩鎳犻鈧。娲⒑鐠囪尙绠茬紒璇插€块崺銏狀吋閸滀礁鎮戦梺绯曞墲閻熝囶敊閺囩喓绠鹃弶鍫濆⒔閸掍即鏌涢悢椋庝虎閻撱倝鏌曢崼婵愭Ч闁稿鍊圭换婵嬫濞戝崬鍓遍梺缁樻尰閻熲晠寮婚悢鐑樺枂闁告洦鍋勮闂備焦鎮堕崐鏍偡瑜忓Σ鎰板箳濡も偓閻掑灚銇勯幒鎴濐仼缁炬儳銈搁弻锝夊箛椤斿厠澶愭煙瀹勯偊鐓兼慨濠呮缁瑩骞愭惔銏″闂備礁鎲¢崹鐢电礊婵犲倻鏆﹂柣銏犳啞閸嬪嫰鏌ц箛鎾磋础闁挎稒绮撳铏圭磼濡浚浜畷顖炲锤濡も偓娴肩娀鏌i幋鐐嗘垿宕h箛鎾斀闁绘ɑ褰冮弳鐐烘煏閸ャ劎绠栧ǎ鍥э躬椤㈡洟濮€閻樿櫕顔勯梻浣哥枃濡嫰藝椤栫儑缍栨繝闈涱儛閺佸棗顭跨捄渚剱闁伙附甯楃换婵嬫偨闂堟刀銉╂煛娴h鍊愮€规洘鍨甸埥澶愬閳ュ啿澹嬪┑鐐存綑閸氬顭囧▎鎴濐棜鐟滅増甯楅悡娑㈡煕閵夛絽鍔氶柣蹇婃櫆閹便劎鎲撮崟顓炲绩闂佸搫鑻粔鐟扮暦椤愶箑绀嬫い鎺嗗亾婵炲懌鍊濆娲箮閼恒儲鏆犻柣銏╁灡鐢€筹耿娓氣偓濮婃椽骞愭惔锝囩暤闁诲孩鍑归崹鍫曘€佸Δ鍛亜闁稿繗鍋愰崢浠嬫⒑閸︻厼鍔嬮柡灞诲妽缁傚秵銈i崘鈺冨帾闂佹悶鍎滈崘鍙ョ磾婵°倗濮烽崑娑㈩敄閸涙潙鐓橀柟杈剧畱閻愬﹪鏌ら崫銉殰濡ょ姴绻掔槐鎾诲磼濮橆兘鍋撴搴㈩偨闁跨喓濮寸粣妤佷繆閵堝懏鍣洪柛瀣剁節閺屽秹宕崟顒€娅ч悗瑙勬尫閻掞附绌辨繝鍥舵晬婵﹩鍓氶崐顖炴煟鎼淬垻顣茬€光偓閹间礁钃熼柕鍫濇搐閺嬪牓鏌涘Δ鍐ㄤ粶闁抽攱甯″娲传閵夈儰绮剁紓鍌氱Т閿曘倝锝炶箛鏇犵<婵☆垵鍋愰幊婵嬫⒑闁偛鑻晶顔姐亜椤撶偞绌挎い锔芥尦閺岀喖鐛崹顔句紙濡ょ姷鍋炵敮锟犵嵁濮椻偓瀹曟﹢鎳犻璺ㄦ寜婵犵绱曢崑鎴﹀磹閺嶎厼绠板Δ锝呭暙绾惧潡鏌熼幍顔碱暭闁稿﹤鐏濋湁闁绘ê妯婇崕鎰版煟閹惧磭绠伴柍瑙勫灴閹瑩妫冨☉妤€顥氭繝鐢靛仜閹冲骸螞濠靛钃熼柨婵嗩槸缁犲鏌涢幇顒€绾ф繛鍫濈埣濮婅櫣娑甸崨顓犳濡炪値鍘奸悧鎾诲灳閿曞倸惟闁宠桨绶氶崬璺衡攽閻樼粯娑ч柣妤佺矊鍗遍柤鍝ユ暩缁♀偓闂佹眹鍨藉褎绂掑鍕箚妞ゆ劧绲块幊鍥殽閻愬澧甸柛鈺嬬節瀹曘劑顢橀悢琛″亾椤掑嫭鐓熼幖鎼灣缁夌敻鏌涢悩鎰佹疁闁诡噯绻濇俊鐑芥晜閸撗呮闂傚倸鍊搁悧濠勭矙閹烘鏅€广儱妫旂换鍡樸亜閺嶃劍鐨戝褝绠撻弻锛勪沪缁嬪灝鈷夐梺鐟板槻閹虫劗鍒掑▎鎾崇閹兼番鍩勯崯瀣⒒閸屾瑧顦﹂柟纰卞亞閹噣顢曢敃鈧粈澶愭煙鐎涙绠ラ柛銈嗘礋閺屸剝寰勭€n亝顔曢梺鍝勫暙閻楀棝鎮為崹顐犱簻闁瑰搫绉烽崗灞俱亜閳哄倻鍙€闁哄本鐩獮妯何旈埀顒勫箠閹扮増鏅繝闈涙川缁犻箖寮堕崼婵嗏挃闁告帊鍗抽弻鐔哄枈閸楃偘鍠婇梺璇叉捣閸忔﹢寮婚敐鍡樺劅闁靛牆瀛╃紞鍫濃攽閻愭彃绾х紒顔芥尭椤曪綁顢曢妶鍥╃厯闁荤姴娲﹂幏婵堢礊娓氣偓閻涱噣宕堕鈧痪褔鎮规笟顖滃帥闁哥喎顑夊铏规嫚閹绘帩鍔夌紓浣割儐鐢繝寮€n亶娓婚柕鍫濇噹椤掋垽鏌熼悷鐗堟悙妞ゎ偄绻愮叅妞ゅ繐瀚ˇ褔姊洪崗鑲┿偞闁哄倸鍊垮畷鎴︽倷閻戞ǚ鎷洪梺鍛婄☉閿曘儳浜搁幍顔剧<閻犲洩灏欐晶鏇㈡煟閿濆洦鐒块柕鍥ㄥ姍楠炴帡骞橀崗鍛处缂傚倸鍊风粈渚€顢栭崼婵冩灃闁哄洢鍨归崒銊︾箾瀹割喕绨奸柛濠傜仛椤ㄣ儵鎮欓懠顑胯檸闂佸憡姊圭喊宥夊Φ閸曨垱鏅滈悹鍥皺娴犳悂姊洪幐搴g畼闁稿鍊曢悾鐑藉Ω瑜夐崑鎾斥槈濞嗘鍔烽梺鍛婏供娴滎亜顫忓ú顏勭闁圭粯甯婄花鑲╃磽娴g瓔鍤欓柛鐔侯棎濡垽姊虹涵鍛涧闂傚嫬瀚伴幃鈥斥枎閹剧补鎷洪梺鍓茬厛閸n噣宕曢幇鐗堢厪闁搞儯鍔庣粻鐐烘煛鐏炵硶鍋撳畷鍥ㄦ畷闁诲函缍嗛崜娑溾叺闂傚倷娴囬鏍窗閹烘鐤鹃柣妯垮皺閺嗭附淇婇妶鍛櫣鐎瑰憡绻堥弻鈩冨緞鎼淬垻銆婇梺鍛婃⒒閺佽顫忔繝姘<婵炲棙鍩堝Σ顕€姊虹涵鍜佸殝缂佺粯绻傞锝嗙節濮橆儵鈺呮煃閸濆嫬鈧鈻撻敐鍜佹富闁靛牆妫涙晶閬嶆煕鐎n偆娲撮柟顔光偓鏂ユ斀闁割偅鑹炬禍鐐殽閻愯尙浠㈤柛鏃€纰嶉妵鍕晜鐠囪尙浠紓渚囧枦椤曆囧煡婢舵劕顫呴柨娑樺楠炴绻濆閿嬫緲閳ь剚鍔欏畷鎴﹀箻缂佹鍘藉┑掳鍊愰崑鎾剁磼缂佹◤顏堟偩閻戣棄顫呴柕鍫濇娴犳椽姊洪崨濠勨槈閼瑰矂鏌熼柨瀣仢婵﹥妞藉畷銊︾節閸曘劍顫嶉梻浣瑰濞插繘宕愬┑瀣畺婵せ鍋撻柟顔哄灲瀹曟鎳栭埡浣哥疄婵犵數濮烽弫鍛婃叏閹绢喖鐤柣妤€鐗婂▍鐘绘⒑椤掆偓缁夌敻鎮¢崘顏呭枑婵犲﹤鐗嗙粈鍫熸叏濡灝鐓愰柛瀣閵囧嫰骞掗幋婵愪患缂備胶濯崹鍫曞蓟閵娾晜鍋嗛柛灞剧☉椤忥拷 Home / HAKAN TAKE novels / HAKAN TAKE part 13 HAKAN TAKE part 13 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 16:57 Rilwan yace kiyi hakuri aisha wallahi ansami akasi ne sosai wanda nakeda tabbacin yanzu haka kinsan dalilin dayasa muka 6uya. Babu abinda zaka fadamin yaya bakada wata zance face kauce kauce, a'a Aisha yakamata yazamto kinyi mana kyakkyawar fahimta sannan kuma kisani fa ba yau muke taredakeba duk halinmu kinsani, dakata yaya ni banida wata zance dazan sake sauraranka da ita kawai abinda zan fada muku saidai godiya nagode sosai bisa abinda kukayimin ace anyi kidnapping dina ko ajikinku? Ke kisaurara mana ki bamu damar yin magana Sagir yayi zance cikin bacin rai, kawai ji sukayi ta katse kiran. awwal yadauki wayar yasake kiran lambar sai yaji wayar akashe, ita kuwa Aisha tana gama wayar sai tajuya takalli khairat cikin zumudi gaskiya kawata kin iya hada game yanzu haka natabbata jikinsu gabadaya zai sanyi kuma sai sun nemi gani na nan bada dadewa ba, Allah ko? Kwarai ma kuwa suka tafa sannan suka cigaba da hira, dukansu suka tashi suka tsaya sai zagaye suke acikin dakin sunkasa zama suna ta faman zance kowa da abin dayake furtawa. sagir yace yanzu meye abinyi wallahi zama da khairat nafahimci babu abinda zai sawa Aisha azuciyarta illa tsanarmu. Kaduba kagani fa abinda yarinyar nan take ta furtowa, Rilwan yakatseshi da fadin gaskiya ta fada sabida zancen gaskiya bamuyiwa Aisha adalci ba, babu wanda da tasani sai mu. Alokacinda aka rufemu waye yaje dominmmu? Ita kadaice, Sannan haka muka gudu batareda muntsaya mungama binciken inda take ba yanzu yazame mana wajibi mukoma musameta, awwal yadubesa tareda fadin hmmm idan kace wajibi ne mukoma shin wace irin amsa zamu baiwa mahaifin khairat yayinda yakamamu amatsayin kidnappers na 'yarsa? Hmmm karka damu wannan ba matsala bace zamuje muyi koda kwana 3 ne acan idan yaso saimu dawo kafin mutafi zamu rike masa kudinsa dama dubu dari biyu muka amsa awajensa sannan kuma dole zamu maida masa su sannnan mu roki gafararsa shida 'yarsa idan mukayi haka zamu wanku taas daga idanun khairat da mahaifinta, awwal yarike kunkumi tareda fadin hmmm kwarai dagaske toh amma kai kanada dubu dari biyu ayanzu haka ? .banida amma ina kudaden da muka raba alikacin da muka je gidan doctor haidar muka kwace kudinmu har da karin da mukayi akai, ai mun raba dubu dari shidan kuma kowa nabashi dai dai sabida haka acikin kudin kowa zai kawo muhada mukaiwa mahaifin khairat kudinsa sannan mubashi hakuri. Daganan yabamu Aisharmu kawail Kwarai kuwa idan mukayi haka shikenan Awwal ya amsa Sagir yace very good. Yanzu zan nemi izini awajen oga Sadauki zanje nayi 3 days acan nasan zai amincemin. Haka suka ajiye zance gobe da zasu tafi amma sai da yamma zasu kama hanya sabida basa son shiga cikin garin da rana ido na ganin ido, zaune suke yayinda khairat ta kai Aisha wajen kawarta zainab danyi mata kitso wata sabuwa chapter suka bude na hira tsakaninsu hamma Sani zai dawo kwana biyu masu zuwa zakiga yayana wanda muke uwa daya uba daya dashi yadda muke matukar kama, hmmmm Allah yadawar dashi lafiya Aisha tafada zainab tace oh Sani duniyar Allah ana nan shiru anacan anata karatu, amma nikam fa harna fara mantawa awace kasa yake karatu ma? Ah haba kekuwa zainab kice kinmanta tare fa dake muka rakashi airport alokacin da zai tafi kuma kowane hutu yana zuwa nan yayi hutunsa kafin nan yakoma. Wallahi kuwa namanta shiyasa na tambayeki zainab ta mayar mata da zance yayinda take yima Aisha kitso, a california yake yana karanta law . Dakyau gaskiya abin yayi kyau karatun law akwai dadi sosai sannan kuma akwai riba. bansan meyas ba nikuma sam abin baya birgeni nifa nafison likita khairat tafada hmmm aikuwa ko wanne da amfaninsa, hakane kinsan dad dinmu ne yabashi damar za6en cause din dazai karanta shi kuma sai yaza6i law, da anan kasar yayi diploma sannan yatafi can califonia domin karo karatun. Ah yayi kyau Allah yasa Albarka akaratunsa yazamto mai amfanarwa ne ga Al'umma, Ameeen suka fada sannan ne khairat take cawa Aisha wata tambaya, shin kawata kina makarantar boko kuwa? Eh nayi makarantar boko har nagama jss 3 dina ma alokacin makarantar dake gidan marayu mukeyi kafin nan azo a watsar da makarantar, Ayya Allah sarki amma yanzu kina tunanin komawa makaranta kuwa? Tadanyi shiru sanann tace toh nikam dai inason yin karatu amma dayake babu halinyin karatun dole haka na hakura, zainab tace toh karki damu insha Allahu zakiyi karatu kisaka aranki cewa kin koma makaranta har kinyi degree hmm tadanyi murmushi sannan tace anya kuwa hakan zaiyiwu ma kuwa? Khairat tace bari mukoma gida kigani zan sanarwa Abba na yasakaki ko a ss1 ne kinga ni yanzu ina ss3 sai mu rika tafiya tare dake ko ya kika gani? Toh bakomai dakuwa nayi farin ciki sosai idan haka tafaru. Karki damu insha Allahu kuma hakan zai iya faruwa ba kedai kawai kizuba min idanu. Haka sukayi tadi har zuwa lokacin da aka kammalawa Aisha kitson kanta . Gaskiya kawata kinyi kyau sosai khairat tafada cikin tsokana hmmm. Toh yaukuma tsokanata zakiyi ko? Hmmm kinfa sani bana tsokanarki sabida haka wannan dinma gaskiya ne nafada irin wannan kitson duk inda kika bi samari sun rinka aiko miki sakonnin idanuwansu kenan gashi kuma kina da gashi sosai gani nayi dankwalinki ma baya iya daure dukkan gashin? Uhm khairat gaskiya tsokanar ya isa haka Aish tafada yayinda ta waiwaya takalli zainaba sannan tace kawata kice mata tadena siffanta ni . Zainab tadanyi murmushi sannan tace toh kekuma dama baki iya kallon abuba kin rinka batu akansa kenan. Ehmana dama ai haka nake kuma yanzu ma saina kara fadan wani abu uhm kawalli dan Allah wane irin man gashi kike amfani dashi ? Aisha taace man gashi kuma? aini tunda nake da wayona banta6a amfani da mangashi ba. Toh lalle kuwa Allah yayi miki baiwar gashi Aisha tadan tura baki kadan tareda murmushi daga nan bata sake cewa komai ba. Suka karashi zancensu sannan zainab tarakosu harwaje khairat takira driver dinta yazo yakaisu gida sabida tun lokacin da akayi kidnapped dinta Abbanta yahanata fita ita kadai. Washe gari Rilwan yaje yasami sadauki Agida suka gaisa sannan sadauki yafara yimasa tambayoyi shin jiya kayi chatting da daddare kuwa? Eh nayi, sadauki yace amma basosai ba ko? Rllwan yace eh. Toh yanzu yau zan nuna maka wata hanya wacce zaka farabi domin samun kasonka kaima awannan harkar. Dafarko inaso kashiga 2go kabude account da sunan mace sannan kashiga room kaga yadda ake addin dinta. Haka kuma kayi amfanida sunan mace a facebook kaga yadda ake yimata messages sannan kuma kanemi sabon simcard kabude whatsAp nanma kayi amfani da sunan mace. Bayan kagama wadannan abubuwan sai kabani labarin bambancin chattin din namiji dakuma mace , idan kagama ina ciki. Rilwan yabude 2go yafara aikuwa yanzu shiga Hausa rooom zokaga yadda ake cin cirindo wajen daukansa amatsayin friend messages kuma akai akai gashi ana ta turo mesages gashi kuma chatting na room na fama dasu ne suma nan take abubuwan suka cakude masa duk dacewa yana da sauri wajen typing amma awannan karon sakonni har sunyi masa yawa, azuciyar yace goood i get the point on this. Sannan ya rufe 2go yakoma faceboook yabude account dasunan maikama da sunan dayayi amfani da ita a2go, sannan yahau facebook account dinsa yasaukar da hotunan wata yarinya dayawa , nan danan friend request sama da dari suka bayyana mushi sai dayarike bakinsa tsabar mamaki sannan yace lalle kuwa matan facebook suna fama da samari garori, haba wannan ai garanci ne dazarar sunga mace tadaura hoto nanfa zaka rinka ganin anata comment , bayan yagama wannan sai ya ajiye wancan wayar sannan yabude sabuwar whatsApp dasunan mace yake amfani ta yadda idan kana chat dashi ta facebook idan kace 'yan mata bani lambar whatsAp naki mana bana jin dadin chattin anan nanfa saai yadauki sabuwar lambarsa yabaka sannan kuje whatsAp dinma kuyi dashi bazaka gane cewa ba da namiji kake chattin ba. Idan kakira lambarsa sai yasauya murya kasancewar yalakanci yadda zaiyi magana irin na 'yan mata. Wannan kenan kadan daga cikin aikin dan yahoo , yagama yaje yasmi Sadauki yasanar masa sadauki yakarbi wayar yabi duk yakalli chat din da yayi damutane eh kwarai kuwa kagane wannan harkar yanzu abubuwan da suka rage maka sune mafi wahala kayi kokari kasan yarukan computer programming language sannan kuma ka koyi yadda ake zana websites sannan kuma yakasance kakoyi yadda ake kutse acikin kwamfutoci, sannan kuma zaka koyi hada software application daku ma virus musamman na computer duka wadannan abubuwan inaso kahadasu kakoya acikin sati daya rak? Sabida haka, zan baka wasu shafuka wadanda zakashiga su dan nuna maka yaren computer dakuma yarukan gina shafin website, idan kaje gidan kabude http:// www.w3schools.com idan kashiga zakaga ababen da suke koyarwa daga ciki akwai yaren gina shafi musamman Html wannan shine ake kira backbone that give every webpage structure shi Html kenan means hypertex mark- up language ina fatan ka fahimta tunda nasani kayi karatu kuma kana da fahimtar da zaka iya koya dakanka balle ma suna amfani da examples sosai acikin shafin sannan kuma tizag,com suma babu laifi kana iya koyo acikinta kamar w3school ina fatan kagane Rilwan ya gyada kai alamar eh nanfa sadauki yace toh yau dama inaga dawuri zamu tashi. Sabida haka idan kaje gida kayi abubuwan da sanar maka sannan kuma gobe kazo da wuri sai alokacin Rilwan yatuna tafiyar dazaiyi yace oga inaso zanyi tafiya zanyi 3days sannan kuma zandawo. Sadauki yace toh babu damuwa amma katabbata kadawo a 3 days din kamar yadda kafada sannan kuma ko acan karka dena karanta abubuwan da cema kana yi, Rilwan ya amsa toh nagode oga Rilwan yatashi zaitafi sadauki yace tsaya mana yazaka tafi haka kawai Sadauki yashiga ciki yafito masa da iphone da kuma nokia c3 sannan yace masa kaje kayi amfani da wadannan kafin kadawo. Rilwan yakar6a cikin girmamawa sannan sadauki yadauki Naira dubu goma yabashi yace kasha ruwa ahanya , Rilwan yayi godiya sannan yakama Hanyar gidan alokacin misalin karfe 3;30 yashiga har cikin dakin alokacin su Sagir basu dawo ba Sabida haka kawai Rilwan yakwanta yakunna wayarsa yahau net kamar yadda Sadauki ya umarceshi dayayi. Yana cikin yi saigasu Sagir sun dawo yauma da nama suka zo acikin jarida anade. Suka zauna suka cinye tare kaf Rilwan yatambayesu yauma matar ce tasaya muku naman suka amsa eh amma yau har cikin gidanta ta kaimu muka zauna da ita ta dafa mana abinci mukaci sannan muka tayata hira gaskiya matar tana da kirki kuma bata kin mutane amma ni abinda yafi bani mamaki shine yadda naga batada miji awannan gidan sannan kuma batada wani da babba ko 'ya ko me dalili oho amma nikam dai wannan matar tana da kirki dakuma kyauta da muka tashi dawowa tabamu kudi Naira dubu shida shida, hmmm Rilwan yayi ajiyar zuci sannan yace gaskiya irin wadannan fa abin tsorone wallahi saidai Allah yakiyaye kawai. Awwal kai mu bamu cema kana cikin aikata abin tsoro ba sai kai zaka fada mana haka? Hmmm Rilwan yadanyi dariya sannan yace ni ai nawa daban ne dukda haka dai saidai muce Allah yakremu. Suka amsa ameeen. Washe gari suka yini agida suna shirye shirye damisalin karfe biyu da rabi abayan sallar azahar suka kama hanyar Adamawa kai tsaye. TAKE novels / HAKAN TAKE part 14 HAKAN TAKE part 14 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 16:59 Ana sallar isha suka iso kasantuwar motarsu akwai gudu sosai, abakin tasha aka saukesu suka fita suka yi sallah amasallacin bakin tasha sannan suka nufi gidan Lauwali kai tsaye, suna zuwa sukayi sallama lauwali yafito muryar waye nakeji kamar su Rilwan, eh wallahi mune haba Rilwan ina kuka shiga haka? Angane Aisah tayi ta jimamin rashin ganinku kullum tana cikin damuwa ina kuka je? Yasake jefa musu tambayar, Rilwan yadanyi ajiyar zuci sannan yace zamuyi maka bayani amma yanzu kafin nan ina Aisha? Lauwali yadan saukar da lumfashi sannan yace muje nima zanyi muku bayani yanzu kuzauna ku huta bari akawo muku abinci zanzo nasameku, toh suka amsa, lauwali yashiga daki yana toh madallah ai gara da kuka dawo din amma fisabilillahi kuntafi kunkyale yarinya ita kadai bayan kunsaba ai haka baiyi ba yana shiga daki yana zance matarsa ta katseshi maigida menene kake ta zance kana tafiya cikin zumudi? Ah wallahi dolene nayi haka kinga yaran nan sun dawo ko ina suka je oho. Matarsa tace ikon Allah bari naje nadubasu lauwali yace dakata ina fatan akwai sauran abinci ko? Tace eh akwai yace yawwa toh saiki zuba musu kije musu dashi daga nan kya dubasu din. Tace toh, taje tasamesu sannunku da dawowa yarannan ina kuka shiga duk kun bi kun daga mana hankali? sagir yadanyi murmushi sannan yace ke kuwa maman Ahmad dan kawai bama nan sai ku bi duk kutada hankalinku sai kace kashemu akayi? Hmm lalle kuwa bakuga yanda kanwarku tashiga damuwa bane shiyasa, inasu fatima suke? Tace sunyi bacci ok toh dama tsaraba muka kawo suka fitar da kayakin dasuka kawo sannan suka bata takar6a sannan ta tafi bayan sungama cin abinci lauwali yazo yasamesu nan suka kwashe labarin abinda yafaru tsakaninsu da khairat sannan kuma da dalilin dayasa suka gudu sannan suka sanar masa cewa sun je neman kudi ne ajalingo kuma suna samun rabonsu. Hmm lauwali yayi ajiyar zuciya sannan yadanyi musu nasiha daga bisani yace musu zai rakasu gidan Alhaji Haruna idan suka tashi zuwa can. Haka dai suka cigaba da hirarsu kusan karfe 10 na dare sannan suka tafi gidan da aka kama musu haya suka shiga dakinsu suka kwanta, Ayau ne Sani Babban dan Alhaji Haruna zai dawo daga carlifornia bayan kammala karatunsa dayayi acan, sabida haka duk suka zauna cikin shiri sannan suka shirya gidan tsaf tsaf sabida sun san Sani dan gayene ya tsani yakalli abu mai kazanta kuma gashi da kyankyami. Aranar duk suna cikin farin ciki khairat tafi kowa murna sabida batada wani dan uwa mafi kusanci kamar Sani bugi da kari wannan shine dawowanshi nakarshe domin yagama karatunsa acan sabida haka yasa tun saura wata 1 yadawo ta keta kirgen kwanaki harzuwa yau ana ranar dazai dawo tun abin baidami Aisha ba amma sabida yadda taga Khairat taketa zumudi shiyasa itama dafara daukin ganin yayan khairat, misalin karfe 9 nasafe Aisha suna zaune a farfajiyar gidan suna ta tadi khairat tana ta bata labarin yayanta dakuma irin yadda takejin dadin zama kusa dashi ji sukayi ana kwankwasa kofa maigadi yafito tared lekawa sannanyace su wayene? Mutane hudu yagani suna tsaye yace musu daga ina? Alhaji yana nan tambayar da suka fara yimasa kenan, yana nan su waye za'a ce masa? Kace masa ana yimasa sallama awaje kawai maigadi ya amsa toh sannan yakama hanya yanufi parlon Alhaji kai tsaye khairat tace masa Baba maigadi suwaye ke kwankwasa kofa? Yace wasu mutane ne wai Alhaji suke nema. Khairat tace Baba kamanta ne ai Abba sun tafi shida driver zasu dauko Hamma Sani a airpot dazu yakira yace sun kusan sauka, hakane fa ni ai har namanta maigadin yafada yayinda yake magana cikin barkwanci hmm su Aisha da khairat suka fara yimasa dariya tareda tsokanansa tsoho mai mantuwa yanzu da an bude musu sun shigo daga ciki idan yaso sai aje akira musu shi ko khairat tafada? baba maigadi yace hakane yaje yabude kofar suka shigo. ganinsu yasa gabadaya suka tashi tsaye lauwali maishago ne yafara shigowa yayinda su Rilwan ke biye dashi abaya, yaa Rilwan Aisha tafada sannan khairat ita kuwa takallesu tadanyi murmushi sannan azuciyarta tace good yayinda takare musu kallo Rilwan sanye yake da riga t-shirt fari dakuma jeans dark blue idanunsa yasaka farin glass wanda kana iya ganin tsiraicin idanunsa afili, Auwal shirt colar yasaka longslief tareda bakin wandow trowser sannan yasaka takalma sau ciki. Sagir polo t- shirt yasaka tareda wandon jeans akafarsa kuma takalman snickers yakuma toshe idanunsa da bakin glas dukdacewa glass din batada fadi sosai amma ba'a iya kallon kwayar idanunsa, Aisha take Hawaye suka bayyana a idanunta batareda ta shirya ma fitowarsu ba, ita kuwa khairat kallonsu kawai takeyi alokacin sai kuma taji zuciyarta yana karaya bisa dukkan alamu kwarjini yashigesu ko meyasa yanzu taji jikinta yayi sanyi game da su ita ma batasan amsar ba. Aisha tana kuka taje tafadi ajikin Rilwan baisan lokacinda shima Hawaye suka fara ambaliya a idanunsa ba yayi ta maza yataresu sannan yajanyeta daga jikinsa yace taje takuma rungumar Awwal shima dai sai da yazubar da kwalla sannnan yajanyeta daga jikinsa Sagir tazo tafada kansa shi kam ko kyar da idanunsa baiyiba amma alamomin tausayinta sun bayyana afuskarsa, yadubeta sannan yace my sister kiyi hakuri kiyafe mana abinda mukayi miki tabbas bamu kyauta miki ba, bata iya bashi amsa ba lauwali yakatsesu yayinda yatambayi khairat batun Alhaji ta amsa masa cewa bayanan amma yakusan dawowa. Rilwan yakalli khairat suka hada idanu sai yasaukar da idanunsa yana kallon kasa batareda takara wani zance ba tace ku iso ciki kai tsaye tawuce dasu cikin babban parlon gidan sannan ta shiga ta kira Hajiya tace mata yayun Aisha sun zo sabida haka taje su gaisa Hajiya tazo suka gaisa sannan takawo musu drinks tazuba musu suna zaune Aisha haryanzu takasa yimusu magana, ji sukayi dirin mota sukaji alamun Alhaji yadawo khairat tafito aguje taje ta rungume Sani tana masa oyoyo yace oh my world best sister sai girma kike ta karawa, khairat tadanyi murmushi tace ai kaima gashinan sai girma kakeyi Hamma ai yanzu kam dolenka Aure zakayi dan nasan ka da cin tuwo tun da can balle yanzu yanda naga tumbinka yadan kumbura gaskiya nikam ummata bazata rika daukar nauyin girka ma wannan cikin naka abinci ba yace ke ni dinne mai katon tumbi ko yakaimata duka cikin wasa tabar wajensa da gudu ta6uya abayan Babanta yace toh kun fara ko? Ke gama neman tsokana gareki tace ai gaskiya nafada masa ai. Yace toh mushiga ciki. Suna tafiya cikin farink ciki khairat tace yawwa Abba yayun Aisha sunzo yanzu haka ma suna falo tareda umma Alhaji yace toh madallah yayi kyau, suka shiga tareda sallama suka amsa musu alokacin suna zaune afalon hajiya da lauwali maishago dakuma su Rilwan, Alhaji yakarasa yasamu waje yazauna ita ko Hajiya ta tashi taje ta tarbi danta Sani kai tsaye khairat tawuce dashi cikin dakinsa dan baitsaya jin meyafaru ba sabida abin bai damesa ba, Itako Aisha tabisa da kallo khairat ta kawo masa abinda ta tanadar cikin dakinsa sannan tace masa zataje falo tasami su Abbanta akwai maganar da zasuyi mai muhimmanci idan suka gama zata dawo. Yace kodai ankawo goron auren kine kuka boyemin tawani daka masa harara sannan tace Allah banaso Hamma. Yace toh shikenan jeki. Sannan tafita daga dakin tazo tasamesu afalo adaidai lokacin lauwali yana yi ma Alhaji haruna bayani. Alhaji wato yaran nan akwai wani abu wanda suka aikata alokacin suna cikin damuwa shiyasa suka gudu alokacin da sukaji kana nemansu kuma har ga Allah sunyi nadamar abinda sukayi maka shiyasa ma yanzu suka zo baka hakuri Alhaji yakalli lauwali cikin rashin gamsuwa nikuma wane laifi sukayimin? Bana tunanin sunyimin laifi kai ko da akwai laifin da sukayimin ma nayafe musu, gabadayansu kansu akasa yayinda dukkansu sukayi shiru acikin falon, Alhaji yadubesu wanne laifi kukayimin yan samari? Awwal yace Alhaji kayi hakuri bakai kadai mukayiwa laifi ba, harda 'yarka musammman ma ita, Alhaji yadaga kai yakalli khairat itako tasaukar da kanta kasa batareda tace uffan ba mekukayi mata Hajiya tajefa masa tambaya. Sagir yace Hajiya kiyi Hakuri nasan abin zai baku mamaki, idan baku manta ba akwai lokacin da akayi garkuwa da khairat sannan aka tilasta muku kai kudi kafin nan asaketa Alhaji kuyi hakuri mune muka aikata wannan danyen Aikin, alokacin idanunsa suka tara ruwa aciki.sannan kuma tun alokacin da ka kiramu awaya harmuka kashe munzata 'yarka taganemu ne kuma ta sanar maka shiyasa kake nemanmu sabida haka ne yasa muka gudu muka bar gari kuma Alhamdulillahi yanzu mun kawo maka kudinka damuka tilasta maka kabamu shi duka a 'yan kwanakin da muka fito daga gidan yarin nan. Alhaji yayi ajiyar zuci sannan yace Allah shine abin godiya kuma shike shiryar da bawansa ta hanyar dayaso hakika naji dadi yadda kukazomin da wannan batun nikam har ga Allah nayafe muku kuma kudin da kuka nema kurikeshi yazama naku halal dinku nina baku shi haka kuma yanda kukace kar na saka 'yan sanda acikin lamarin haka bansaka su ba har yau na rufe maganar yanzu tunda Allah yasa kungane cewa kuskure kukayi wannan shine abin farin ciki. Mongode sosai Alhaji Allah yabar zumunci. sannan Rilwan yadubi khairat dan Allah khairat kigafarcemu bisa abinda muka aikata, adaidai lokacin Sani yashigo zancen ne ta doki kunnensa , " dan Allah khairat kigafarcemu abinda muka aikata" idanunsa akansu Rilwan har yakaraso yazauna sannan yakasa kunne domin jin abinda yake gudana awajen, khairat tace babu komai na yafe muku. Sukayi godiya sannan ne lauwalli yace ma Alhaji toh Alhaji yanzu yayun yarinya sunzo kar ayita daura muku nauyi idan zaiyiwu ku mikata ma yayunta idan yaso su zauna tare khairata ta daka masa Harara sannan tace gaskiya babu inda Aisha zata je sabida muna jin dadin zama da juna. Alhaji yace ke aka tambaya ne? Ai 'yar uwansu ce sabida haka idan suna son tafiya da ita babu wani damuwa zasu iya tafiya tare, lauwali yadubi Aisha sannan yace shin ko zaki koma wajen yayunki? Saukar da kanta tayi batareda tace komai ba bisa dukkan alamu tarasa inda zata za6a, sai alokacin Sani yakalleta , nan yakura mata idanu yagama daukar kamanninta awajen tabbas wannan yarinyar tanada kwarjini azuciyarsa yafada hajiya ta hangoshi tace kai dan nan me kake gani kamanta bakinka abude Haka ? Dasauri yarufe bakinsa sannan yakawarda idanunsa daga kanta, Awwal ne yafara maga toh Alhaji idan har zata zauna anan babu wani damuwa zamu iya barin ku tareda ita su zauna da khairat har zuwa wani lokaci, khairata tadanyi murmushi bisa dukkan Alamu ta ji dadin zancen Aisha zata cigaba da zama tare da khairat agidan, bayan sun gama zance Rilwan suka tashi zasu tafi Sani yamika musu hannu suka gaisa da kowannensu sannan suka sake godiya ma Alhaji daga bisani suka ce zasu tafi amma gobe zasu dawo. Har sukoma zasu rika zuwa suna ganin kanwarsu. Suka fito har waje su khairat sukayi musu rakiya har bakin kofa sannan Alhaji yahadasu da driver yace yakaisu gida, Suka dawo gida hankalinsu yakwanta Rilwan yafitar da wayarsa kawai yahau net. Su Aisha kuma bayan sun dawo daga rakiyar khairat takama hannunta tace tarakata zuwa dakin hamma Sani suje suyi tadi dashi dan tasan baya rasa hira musamman ranar daya dawo yaka zauna yayita bata labarin kasar waje, kai tsaye suka shiga cikin dakin yayinda Suka samesa yana kwance acikin daki singileti ne ajikinsa dakuma wando tracksoop, Hamma mun kawo maka hira na musamman yau nida kawata. Dasauri ya waiwaya yakallesu sannan yayi murmushi toh sarkin damuwa duk lokacin da na dawo sai kin fitineni da surutu. Au wato hamma nice zaka kora yau ko? Kamanta kenan duk lokacin daka dawo kai da kanka kake nema na muzauna kayi ta bani labari ko? Yadanyi murmushi sami waje kuzauna albarkacin kawar taki dan naga kamar tafiki hankali.Aisha tadanyi murmushi batareda ta ce komai ba. Sannan ne Sani yatuna yace yawwa dazu naji wani daga cikin mutanen da suka tafin nan suna baki hakuri shin wai me sukayi miki ne? Tace toh bakace zan dameka da surutu ba toh nima bazan fada maka abinda sukayi min ba. Yace kinga sister wasa fa nake miki dan Allah kifada min tace sai dai kaje katambayi abba ko mama amma nikam bazan fada maka ba. Yace toh ai ga kawarki nan kusa. 'yan mata ya sunanki? sani yatambaya yayinda yakura mata idanu kyanta ya bayyana afili Sani yana kare mata kallo tace sunana Aisha yace Aisha gaskiya Aisha kina da kunya sosai bakya iya kallon mutum idan zakiyi mishi maga kome yasa hakan? Tadanyi murmushi sannan tace babu komai ni haka nake. Yace hmm gaskiya nikuma bansan meyasa ba duk me irin haka sainaji yana matukar birgeni sosai bakamar khairat ba idan tafara zance kamar ankunna Radio.HAKAN TAKE novels / HAKAN TAKE part 15 HAKAN TAKE part 15 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 17:01 Khairat tadan zumbura baki ai duk surutun da nakeyi awajenka nakoya sabida haka bakada bakinda zakacemin idan ina zance kamar ankunna Radio. sani yace toh dai ba wannan ba, ban mance da tambayata ba meyafaru wadancan mutanen suke bata hakuri malama Aisha bani amsa? Aisha tadaga kai takalli khairat sai ta fahimci khairat tana gyada mata kai alamar karta fada, sai Aisha tace nima bansani ba, yadan juya yakalli khairat sannan yace kinsan Allah zaki barnan ? Tace toh basai ka koreni din ba dan kasamu ma anzo wajenka . Toh tashi kibarmin daki Khairat ta tashi cikin fushi takama Hannun Aisha yayinda take zaune kitashi mubar mishi dakinsa tunda korarmu yakeyi, Aisha kamar bazata tashiba tatashi Khairat tana janta tafara murmushi ke Khairat me hakan nace kitafi da ita ne? Ni ke kadai nakora ba ita ba tunda ke baza'ayi zancen Allah da annabi dakeba. Ai kawata ce kuma tare kaganmu kuma haka zaka kyalemu suka fice daga dakin Yabiyosu. Ke Khairat zan sa6a miki fa? Ko kulashi batayi ba tafita daga cikin dakin suka wuce dakinsu kai tsaye yabiyosu yana tsaama khairat da taji zuwansa sai taje ta rufe kofar dakin sannan tasaka sakata ta ciki. Yazo yatsaya abakin kofar ke Khairat kizo kibudemin inba hakaba zan balle kofar dakin nan fa? Tace ba ka koreni adakinka ba nima bazaka shigomin daki na ba, hmmm yagyada kai yajuya zaki fito ai sai nayi maganinki aransa yafara raya zance khairat kam yaushe zata girma ne? kaduba yarinya kyakkyawa ko 'yar gidan waye tasamu oho bisa dukkan alamu kuma yarinya akwai hankali. Kai tsaye yawuce dakin Hajiya yaje yasameta tana shirya kaya a wardrof , yayi sallama sannan yashiga kai tsaye yasami waje yazauna, tace masa Yaya dai Sani lafiya kuwa bakace kana da wasu ayyukan dazakayi su ayanzun nanba? Yace Eh wallahi umma dama nazo tambayarki ne. Tace toh menene. Yace Umma dazu nasameku da wasu mutane afalo sai kuma naji daya daga cikinsu yana cewa Khairat ta yafemusu anan na fahimci cewa akwai wani abinda yafaru sannan kuma natambayi Khairat taki fadamin, tadanyi Murmushi Sani kenan yo kaima in banda abinka yaza'ayi khairat ta fadamaka wannan zancen ai wannan zancen badai kajishi abakin Khairat ba. Yace umma toh wane irin zance ne haka? Tace kaganmu nan nida mahaifinka kafin tafada mana wannan zancen sai da mukayi da gaske. Yace ina fatan dai ta fadamuku din ko? Tace Eh yace toh umma ina sauraronki menene yafaru tsakaninsu, nan Hajiya ta kwashe bayanin abinda yafaru duka ta sanar ma Sani, sannann yadanyi shiru yana nazari daga bisani ya kuma tambayarta Umma akwai wata yarinya dasuke tareda Khairat ita kuwa 'yar waye ne? Hajiya tayi murmushi sannan tace nasan dole katambayeni batun wannan yarinyar domin nalura tun da kazo idanunka akanta, yadanyi sosa kai tareda murmushi, nan Hajiya takuma kwashe labarin Aisha kaf tasanar masa, take yaji tausayinta yashigeshi jiki asanyaye yayiwa Hajiya godiya sannan yatashi zai fita Hajiya tace saura kuma ayi zurfin ciki. Yajuya yace umma zurfin ciki kuma cemiki nayi ina sonta? Hajiya tace au ka tsaneta kenan? Sai kuma yayi shiru, tace inajinka idan katsaneta sai muji. Yadan sauke murya Umma dan Allah ki rufamin Asiri ni inada wacce nakeso kuma munyi alkawarin Aure da ita sabida haka kar ma kisa yarinya tafara sakani cikin ranta, hajiya tayi murmushi tace toh jeka shidai ido ba'a nuna mishi bacci, yajuya yatafi duk atsarge yaje yakwanta adakinsa sanann yacigaba da wasu rubuce rubucensa, abangarensu Rilwan kuma bayan sun koma gida Sagir yake cewa Nikam nakalli wani gaye a gidansu Khairat fa kodai shine yayannata? awwal yace Shine inaga yadawo daga kasar waje ne domin kuwa ba'a nan kasar yake karatu ba. Kai gaskiya gayen balaifi yana da sakin fuska. Hmmm ni na fahimci ma sai kallon Aisha yake ta yi kome dalili bansani ba Sagir yafada. Awwal yace hmmm wayasani dama ai samari duk inda sukaga budurwa kasan basa iya kifta idanu sai sun karemata kallo kamar yadda kaima kakeyi yamayar masa da amsa, kai fa baho ne Sagir yafada sannan yace ai kallonma iri iri ne. Shifa kallon dayake mata zakace akwai wani abu dayafaru tsakaninsa da ita. Hmmm wancan gayen fa baya kula 'yan mata danni inada full historinsa tun kafin mu tuna cewa zamu sace khairat. Rilwan shiko yana kishingide akan gado yayinda yake chatting a WhatsApp. Awwal yace kai sarkin chat idan kayi wasa fa zaka mutu da waya ahannunka. Rilwan yace hmmm ai ni abinda zai rabani da social network sai mutuwa. Toh idan kamutu ai shikenan sai akaika abinneka da waya har kabarinka din kayi chattin acan sagir yafada. Hhhhh yadanyi murmushi kai nifa ko alahira idan ace nasamu daman shiga aljannah sai nayi chattin acan, kai fa zakayi sa6o fa awwal yakallesa tareda katseshi bawani sa6o azancen nan yamaida masa magamana, Sagir yace toh acan kuma ina zakasamu su facebook da sauransu? Rilwan yace haba ai aljanna duk wani kayan more rayuwa dakasani aduniyar nan akwai toh akwaishi acikin ajannah sabida haka sai munyi chattin idan muka shiga aljannah, hmmmm a ina zakasamu friends awwal yatambayesa. Yace akwai friends kai gashi kuma zanyi chattin da matan hurul aini wadanda babu ruwana da binsu ta inbox ina cewa hello,hi, xup,slm. Suna ta renamin hankali baruwana da turawa mata friend request sai dai suturomin sannan kuma idan nayi accepting dinsu sucemin thanks for accepting my request. Hhhhhhh lalle kuwa kasami matsala.. a ina kenan zakasamu wannan saken sagir yalatseshi da zance Rilwan yace acikin aljannar mana, hmmm wannan mahaukaci ne Sagir yafada sannan yajuya gun awwal yace muciga ba da hirar mu kaikuma kayi ta chatin dinka kawai. Can dayamma rana tayi sanyi suka yi wanka suka fito suna zagayawa acikin gari suna gaisawa da abokan arziki, suna tafiya suna jajantawa gaskiya matasan garin nan akasari basuda aikinyi Rilwan yafada sagir yace ahakanma yanzu da yamma ne akasari sun tafi filin kwallo da ace da rana tsaka kazo zakasha mamaki idan kaga yadda ake zama daga karta sai musanyar zance sai fadace fadace, toh Allah yakawo musu aikinyi Awwal yafada suka ce ameen sannan suka wuce, washe gari dasafe suka je gidan Alhaji Haruna suka gaishesa yaukam sun sami sakin fuska awajen mutanen gidan gabadaya musamman khairat dan haba haba take dasu sai kuma Aisha inda tasake suna zance tamkar yadda suke abaya, haka shima Sani yafito yasamesu afalo suka kafa hira. Suka jima suna tadi nanfa Sani yakar6i lambobinsu alokacin suke sanar masu Aisha cewa gobe sukeso zasu koma taraba, Aisha hankalinta sam baikamaba sabida ta san halinsu azuciyarta take cewa Allah yasa dai ba wani barna suke aikatawa acanba, misalin karfe shabiyu aka kawo musu abinci sukaci sannan suka ce zasu tafi sai gobe kafin sutafi zasu biyo tanan suyi musu bankwana. Khairat tace dan Allah inaso nayi zance daku anjima idan babu damuwa dayamma kuzo mugana, Sani yace wane irin ganawa ne bazakuyi yanzu ba, Aisha tace nima dai haka nagani khairat tace babu ruwanku tsakanina da mutane na muke zance kuma idan kukace zakuyi mana shishshigi sai ince su sake kidnapping dina muje wani waje mutattaunan, duka suka tuntsire da dariya sannan Rilwan yace a'a baza'ayi haka ba ai mundena kidnapping dama ke kadai muka ta6a sacewa kuma daga kanki bamu sake dauke kowa ba sabida haka zamu dawo anji ma din, khairat tadanyi murmushi sannan tace yawwa Rilwan suka fita suka kama hanya sai gida aranar suka dan yi shirye shiryensu zuwa yamma suka yi wanka sannan suka je gidan Alhaji haruna, acikin farfajiyar gidan suka sami su khairat su 3 Aisha da kuma wata buddurwa wacce basu santa ba, awani dan karamin runfa suke yayinda suka karaso wajen kamar daman anshirya musu wajen ne kujeru uku babu kowa akai sannan an ajiye musu kayan abinci agaban kowanne kujera, bayan sun iso khairat ta nuna musu wajen zama suka zauna sannan Rilwan yace malama khairat kinga muncika alkawari ko? Tace eh tabbas kun cika alkawari Rilwan yajuya gefe yakalli Aisha sannan yace toh kekuma sai da kika zo jin zancen dazamuyin ko? Khairat tace ai da ita muka shirya wannan zamar awwal idanunsa akan dayan budurwar bisa dukkan alamu atakure take tagama fahimtar kallonta yake sagir kuma yafara cin abincin da aka tanadar musu yayinda shikuma Rilwan tadinsu sukeyi da khairat ita ko Aisha sai sauraronsu take, khairat tace bakuga bakuwa bane? Rilwan yace nakalleta amma kamar zanyi miki batunta sai kuma naga awwal yanace da kallonta shiyasa nayi shiru kar nayi masa cikas sai alokacin awwal ya ankara sannan yakawarda idanunsa cikin kunya nanfa suka kama yimasa dariya, khairat tace kawata ce tunda muka fadamata yayun Aisha sunzo take cewa tanaso taganku nikuma naji kunce gobe zaku tafi shiyasa nakirata yau nasanar mata tazo. Rilwan yadanyi murmushi sannan yace malama ya sunanki tace sunana zainab yadanyi ajiyar zuci malama zainab kuyi zancenku da awwal naga kamar akwai maganar dayakeson fada miki. Sagir yakatse Rllwan dacewa haba kaifa kasa Awwal din nan agaba bayan kasanshi tsoron mata ne dashi suka kuma tun tsirewa da dariya zainab tace a'a gaskiya abinda kukayi masa baidace ba shikenan kuma dazarar yayi abu sai kurika yimasa dariya, Aisha tace hmm yo mema kika gani idan wadannan yayun nawane ai duk wanda yakofsa acikinsu ko a inane dariyar mugunta suke masa, Awwal yatashi ransa abace nida nasan dalilin kenan da yasa khairat tace muzo da wallahi bazan zoba . Hmmm karka damu zainab tafada bani lambar wayarka kafin katafi yadanyi shiru tareda cewa lambar wayata kuma? Tace eh, kafin ya ankara kawai yaji Rilwan yana cewa kisaka 080 yakira mata lambar awwal duka sannan tayi saving awwal yakaima Rilwan bugu Rilwan yakauce yatashi yana yimasa dariya, haka suka yi ta tadi har dare kafin nan suka koma bayan sun koma sagir yake cewa Rilwan nikam wai me tsakaninka da khairat ne naga fa tasaki jiki sosai da kai? Rilwan yace babu komai mekagani daga waje Awwal yake cewa karyane akwai soyayya atsakaninsu Rilwan yatashi ransa a6ace wallahi awwal ranka zai 6aci ni bana soyayyah sai dai abota kodayake kome kafada bazan damu ba sabida yau nahada ka yarinyar da kazurawa idanu kamar wani mai duban watan sallan azumi, hmmm nifa yarinyar can batayimin ba awwal yafada Toh nima Khairat batayimin ba Rilwan yafada. Duk kugama zantukanku nasan abinda ke damunku kuruciyane sabida haka karma kufara saka mata acikin al'amarinku tunda nasan yanzu kam ba aure zakuyi ba idan kuma kukace zaku shiga soyayya toh wallahi idan kukayi wasa kome kuka sa agaba sai ta rushe Sagir yafada. Hmmm toh wayema zai fara shiga soyayya ni banda hankali ne Rilwan yamaida masa martani au wato nine mahaukaci da kuke faman jefani cikinta ko? Toh sam baziyiwuba awwal yafada, washe gari dasafe suka shirya sannan suka je gidan lauwali sukayi bankwana dashi da matarsa sannan suka sayowa su Fatima da Bilal kayakin sawa suka bawa lauwali Naira dubu hamsin sukace yasaka fatima da Bilal amakarnata Lauwali yace su bar kudinsu zai sakasu da kudinshi sabida yanzu yadaukesu ne amatsayin 'ya'yansa, Sannan sukaje gidan Alhaji Haruna suna gaisheda su sannan suka sanar musu tafiyar su Alhaji yadauki naira dubu ashirin yace su sha ruwa ahanya suka ki karba Alhaji ransa a6ace yatilasta musu kar6a har suka fita godiya sukeyimasa Aisha idanunta suka ciko da kwalla Rilwan yakarisa inda take sannan yace haba Aisha mehaka kiyi hakuri kinji bawai mutuwa zamuyi ba zamu rika zuwa kina kallonmu sabida haka kidena daga hankalinki alokacin Sani yakariso wajen Rilwan yamika masa hannu suka gaisa Sannan yace hamma Sani ga kanwarmu munbarmuku ita amana dan Allah kurike mana ita amana Sani yadanyi murmushi sannan yace karkadamu insha Allahu zamu kula da ita yadda muka dauki khairat agidan nan bazamu bambanta su ba, Rilwan yayi godiyan sannan dubi khairat yace khairat babu abinda zamu iya ce miki saidai Allah yasaka miki da Alheri Allah yabar zumunci mungode tadanyi murmushi Allah shine abin godiya, suka dauki Naira dubu ashirin suka bawa Aisha sukace tasayi waya dashi sabida surika gaisawa ta karba sannan sukayi addu'an Allah ya kiyaye hanya, daga bisani suka nufi tasha suka shiga mota kai tsaye suka doshi birnin jalingo.KE part 16 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 17:02 da misalin karfe 5:30pm suka iso kai tsaye suka doshi camp lovet hotel suka sami masauki sabida ayanzu sunsan kan garin. Rilwan yakira Sadauki awaya yasanar masa cewa yasami dawowa sabida haka gobe zaizo sucigaba da harka. Sadauki yace masa toh bamatsala don't forget to come with my tsaraba Rilwan yayi murmushi yace ok oga badamuwa, washe gari da safe Awwal da sagir Suka fito suna yawatawa agari har suka iso wajen mainama inda suke zama suyi hira, bayan sunyi sallama suka karisa cikin rumfarsa, yadubesu yace 'yan gayu. Ina kuka shiga ne kwana 2 Sagir yace munyi tafiya ne wallahi, mai nama yace da walakin nasan za'a rina ai Hajiya fadila tayita zuwa nemanku anan bata samunku. Gabadaya idan tazo bata ganku anan ba cewa take tanaji kamar tayi asarar wani abu, Awwal yace hmmm ni dama nayi tunanin nan matar nan sai ta tambayemu idan bama nan, Sagir yace toh ko zamuje gidanta ne yau mugaishe da ita? Awwal yace a'a basai munje gidan ta ba idan hajiya fadila ce ita da kanta zakaga tazo nan ai kullum anan take zuwa sayan nama, Sagir yace idan kuma batazo bafa? Kaga yakamata muje mu sameta kawai domin kuwa matar nan tana da mutunci sosai.kar muyi wasaa da lamarinta bamusani ba ko arzikinmu ta fanninta zaizo? Awwal yadanyi shiru sannan yayi ajiya zuci daga bisani yace toh babu komai anjiima kadan sai muje ko? Sagir yace toh babu damuwa suka zauna awajen sukayi hira da menama nawasu 'yan sa'anni daga bisani suka kama hanya kai tsaye suka wuce gidan haijya, alokacin da sukaje sai suka sami kofar arufe sagir yace ma Awwal toh kodai zamu jirata ne nan da anjima kadan Awwal yace a'a nikam babu zaman da zanyi abakin kofar gidan mutum kamar mai jiran kar6an bashi, gaskiya tafiyana zanyi idan yaso sai gobe mudawo, sagir yace toh babu komai sai goben sun juya suna tafiya alokacin sai gatanan ta dawo amotar ta, tadan sauke glass din motar cikin fara'a Sagir kuna nan ma kuwa? Yadanyi murmushi yayinda suka karaso inda take ,eh wallahi Hajiya muna nan kawai munyi tafiya ne, tace ok yayi kyau toh daga ina kuke yanzu, awwal yace dama munzo wajenki ne gaisuwa sai kuma mukaga bakyanan . Toh yanzu sai mukoma ai tunda ganinan nadawo. Kai tsaye suka je suka zauna afalon Hajiya Fadila takawo musu abinci da drinks sukasha. Sai anan take tambayarsu nikam ku meyasa koda yaushe bakwa rabuwa ne? Awwal yadanyi murmushi hajiya kenan ai mu dakike gani tun muna yara atare muke yanzu ne ma muka fara rabuwa sabida mu uku ne yanzu haka ma dayan yatafi wajen sana'arsa ne, nan ta shiga yimusu tambayoyi kamar ma aikaciyar jarida , haka harta fahimci cewa basu da aikinyi sabida haka sai tace yanzu zatabasu aiki agidanta sabida bata cika yawan zama ba zata rika biyansu kudi yanda suka bukata hajiya kenan naga kuma agidan ki din babu wani aiki wanda za'a ce har sai mutane 2 sun hadu kafin suyi aikin. Tace bakomai bane kawai zaku rika kulamin ne da bishiyoyi da kuma fulawowin dake shuke acikin gidan nan sannan kuma ko wannenku zai rika amfani da lokacinsa nadaban idan wannan yayi aiki dasafe har karfe 12 zaikai sannannkuma dayan yazo daga shabiyi har zuwa karfe 6 na yamma, suka amsa mata cewa sun amince. Tace yawwa toh yanzu gobe waye zai fara aiki acikinku? Sagir yace zai fara awwal yace toh babu damuwa sai goben, abangaren Rilwan kuma bayan yaje yasami Sadauki sannan yake cemasa ina fatan kana bibiyan darasin da mukayi ko? Rilwan yace kwarai kuwa duk abinda mukayi ban manta ba, sadauki yace toh bakomai. Ina fatan kashiga w3schools kakoyi HTML aciki? Rilwan yace kwarai kuwa nashiga kuma nayi iya bakin kokari na, Sadauki yace toh babu damuwa ina fatan kayi addin na webmasters acikin friends dinka na facebook ko? Rilwan ya'amsa kawarai kuwa nayi. sadauki yace good ina fatan kana bin links din dasuke yawan ajiyewa ko? Rilwan yace kwarai kuwa ina bi, toh haka nakesonji yanzu tunda kakoyi HTML darasin dazamuyi yau zan fara gwada ka tukunnna sabida haka zan nuna maka yadda zaka bude website irin na wasu daga cikin arewa webmasters dakake gani? Yace toh ina jinka, sadauki yace kadauki wayarka java phone Rilwan yadauki c3 din da sadauki yabashi sannan yasaka simcard aciki. Sadauki yace ina fatan kayi download na uc browser? Eh ina da ita sadauki yace yawwa toh kashiga Uc browser din kaje wajen da ake saka Url sai ka rubuta wapka,com zasu kaika cikin wani shafi anan zakaga wajen login kamar na facebook inda zasuce kasaka email dinka sannan kuma kasaka password dinka akasa kuma zakaga signUp toh sai kashiga sign Up dinnan zakaga sun baka za6uka aciki zakaga akwai inda akace passport toh anan suna nufin email dinka saikasaka musu email dinka idan kuma bakada email saikaje wajen saka url karbuta www.gmail.com idan yabude maka zakaga create account saikashiga idan kashiga zasu ce kasaka lambar wayarka saikasaka musu bayan kasa kafin 1minute zakaji message yashigo maka acikin message din zaka ga wani link aciki saikabi linki din zai kaika har cikin shafin su din zakaga lambarka din amma babu guda biyun karshensu zasuce kacikita lambarka din domin cigaba sai kasaka lambobi biyunda basu zo maka ba, bayan kasaka sai kayi next zasuce maka ka rubuta sunanka bayan kasaka musu zasu nuna maka wasu sunaki wadanda acikine zaka za6i sunan da kakeso zakayi amfani dashi amatsayin email dinka idan kuma duka basu yi maka ba akwai wani box sai kaduba kasaka irin sunan dakakeso amma idan akwai wanda yake amfani da irin username din bazasu baka daman amfani da ita ba sabida haka saika za6i wani sunan bayan kagama zasuce kazabi password dinka da kanka sai kaza6a sannan kuma kuma ka sake maimaitawa shikenan kagama da email sai kaje kayi login na email din kamar yadda kake hawa facebook. sannan kabude tab kakoma shafin wapka,com bayan kashiga signup wajen da aka rubuta pasport wato emai za'a saka awajen kasa kadan kuma password sai kuma kayi comfim password Sadauki yana Rike da waya yana nunawa Rilwan yadda zaiyi sannan kuma zakaga sunce kaza6i site name sai kazabi irin sunan dakakeso website dinka din yazama. Shikenan sai kayi signup bayan kayi signup zasu tura maka comfirmation code tacikin email dinka sannan sai kaje gmail.com zakaga sakonso saika bude akwai comfirmation code sai ka dauka kaje kasaka acikin site dininda sukace ka saka comfimation code din shikenan bayan kasaka zasu nuna maka successfully kabude website, shikenan iya abinda zan nuna maka kenan sauran design din cikin kuma dama ana amfani ne da HTML ne wajen zanawa kaikuma ka iya HTML sabida haka no need na tsaya inata nuna maka sabida haka zakaje ka koya da kanka ahankali sannan kuma kasani bashi kadai zaka koya ba. Bayan kagama dole zaka nemi kasan yadda ake hada phishig site dasauransu yanzu dai abinda zakayi shine design sabida haka kaje kayi dakanka, Rilwan yadanyi murmushi sannan yace toh bari kagani yanzu zanyi nakawo maka. Sadauki yayi dariya sannan yace ai karyanka kazana website cikin kwana 2 koda ka 'iya. Rilwan yasami wajen yafarayi yanata jagwalgwalawa har dare batareda yafitar da abu gud 1 acikin site dinsa mai kyau ba, sadauki yace yanzu yakamata kaje gida sai gobe kadawo amma kafin nan kawo muga abinda kayia din? Rilwna yamika masa yakar6a yagani mai kyau sannan yace hmmm kayi kokari amma fa sai ka kara hazaka wannan abin ba wasa bane sadauki yafada Rilwan yayi godiya sannan yatashi zai tafi sadauki yadauki dubu biyar yabashi sannnan yayi godiya yakama hanya yadawo gida yazauna yayi tayi kusan kwana yayi yana koya amma sam abin dasaura idan yashiga site na wani yakalla sai yaga da bambanci har yagaji misalin karfe 2:30 na dare yakwanta yayi bacci sabida hakane ma yasashi makara shine bai farkaba sai misalin karfe 8 nasafe. Hakan TAKE novels / HAKAN TAKE part 17 HAKAN TAKE part 17 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 17:04 Adayan 6angaren kuma bayan tafiyar su Lauwali yasaka fatima da Bilal amakarantar primary tareda 'ya'yansa. Aisha kuma bayan tafiyarsu jikinta gabadaya yayi sanyi suka zauna cikin daki suna tadi ita da khairat hmmm shikenan sunzo fa harsun tafi din, eh dama ai haka ne duk abinda ake marmarinsa kamar bazaizo ba idan yazo yawuce sai aga kamar baizoba, hmmmm nikam wane sana'a sukeyi acan ne? Khairat tajefamata tambaya, Aisha tace eh toh gaskiya namanta bantambayesu ba amma inada tabbacin kwadago sukeyi, toh koma dai wacce sana'a sukeyi yanzu akwai alamun suna samu acikin sana'ar khairat tafada, aisha tadan ta6e baki nifa hankalina baikama jalingon nan dasuka koma b Sabida inajin labarin garin ana fama da tsagerun mutane. Kedai kawai addu'a zaki rikayimusu Allah yashiryar dasu sannan yasa su kan hanyar daidai . Aisha tace ameeen, washe gari dasafe bayan sunyi breakfast khairat tashirya zata tafi makaranta tasaka Uniform dinta kasantuwar alokacin tana SS3 sabida haka ne yasa kota makara bata damuwa sosai. Sani yazo yasamesu akan dinning table yajawo wani kujera sannan yazauna Aisha tagaishesa ya amsa cikin fara'a sannan yadauki cokali yafara cin abincinsa kekam baki iya gaisuwa bane? Yatambayi Khairat .. Tace namanta ne ina kwana ko amsa mata gaisuwa baiyiba. yaushe zaku fara rubuta waec and neco yajefamata tambaya, tace sai a watan uku zamu fara ok ni kinsan harna manta date din da akeyi, yanzu idan kika tafi makaranta Aisha ita da waye suke zama? Aisha tace nikadai nake zama saidai naje nasami umma nayita tayata aiki, yace kefa bakya makaranta ne khairat tace eh tanayi tagama JSs dama Abba yace zai sakata amakaranta tun last week kuma naga haryanzu shiru baya ko maganar, may be aiki ne yayi masa yawa amma idan kinshirya ko yau sai muje Ayi miki rejista idan yaso daga baya saiki fara zuwa idan kin dinka uniform. Ko Aisha tace eh inaso, yace yawwa toh sai muje tareda khairat idan zata tafi, suka fito tareda Sani driver din khairat yana jiranta tafito sutafi sani yace masa ya huta kawai yau shi zai kaisu yaje yabude motarsa yashiga Khairat tazo tabude tashiga Sani yace kikoma baya Aisha ce zata zauna agaba, Khairat tace ko me dalili yace bansani ba yadoka mata harara ita ko Aisha taje zata shiga baya yace ke Aisha nan zaki shigo ba can ba yafada mata , khairat tadan kalli idanunta Aisha sannan tadanyi murmushi kodai akwai wani abune bari na baku waje ? Aisha tadan tsaya kamar bazata shiga ba bisa dukkan alamu kunya yakamata , kishigo muje mana Sani yakara fada mata. Tadan kalli Khairat sannan tasaular dakanta yayinda taga alamar Khairat tana murmushi. Tashiga tazauna suka kama hanya, ahankali suka fara tafiya babu wanda yayi magana tafiya kawai suke yayinda Aisha tasauke kanta kasa kamar tana kallon wani abu ahannunta. Can Khairat talura da Sani yana Satar Kallon Aisha sai tadanyi gyaran murya dasauri ya ankara yagane abinda take nufi amma dukda haka sai da yadan waiwaya tareda cewa me kike yiwa mutane gyaran murya, sai tace naga kamar kana kallon wani wajene sai kuma naji tsoron karkaje ka wurgamu cikin rami shiyasa nayi maka magana, baisan lokacin da dariya yashigesa ba hmmm zan sa6a miki fa? Tace au menayi kuma zaka sa6amin yace kinfini sani ai tace tam shikenan, itako Aisha batayi magana ba har suka iso makarantar , yasami waje yayi fakin sannan suka sauka yace ma Khairat toh mun sallameki sai ki wuce aji. Tadan zumbura baki ai ba saikafamin ba kullum ina zuwa, yace aje dai ata fama, tarike Hannun Aisha tace ya kikaga makarantar Aisha tace gaskiya makarantar yayi kyau akwai tsari makyau Aisha tabata amsa, tace good ga can ajinmu mune Ss3 Aisha tayi murmushi sanann tace yayi kyau sani yakaraso inda suke ke sake mata hannunta kitafi ko kuma in sa6a miki, Khairat ta saketa sannan tace gaskiya kawata kinsamu bodyguad mai zafin rai bari natafi kar yata6a lafiya na. Nikike cewa bodyguard ko yacire takalminsa ya harbeta dashi ta ruga dagudu tana yimasa gwalo harta shiga aji ita ko Aisha sai dariya takeyi. sani yace mata toh kekuma sarkin dariya muje ko tace toh suka kama hanya kaitsaye suka wuce cikin office akabasu waje suka zauna Sani yagama yimusu bayani suka kar6eta komai sun gama Sani yacire kudi yabasu akace zata iya fara zuwa sannan aka saka sunanta arejista, murna takeyi sosai suka fito tana tayima Sani godiya yace mata gaskiya banaso godiyanki yayi yawa Aisha abu kadan sai kin godewa mutum kefa yanzu kanwatace duk abinda nayi miki kanwata nayiwa , murmushi tasaka sannan tace toh hamma Sani idan banyi maka godiya ba mezance? kigodewa Allah kawai. Ta kara saka murmushi shima yasaki murmushin sannan yace toh mutafi ko tace toh, sukaje suka shiga mota sannan suka kama hanya suna tafiya Sani yake cewa Aisha meyasa ke bakya magana ne? Tace babu. Yace hmmm alamun bazaki iya aikin jarida ba, tace ko me dalili? Yace gashi nan bakya son magana kuma alamun har yanzu baki saki jiki dani ba, tace hamma ai munsaba dakai kusan kullum muna tarefa idan kana gida. yace hmmm hakane kice idan muna tareda Khairat dai kedinda kamar kurma bakyason magana, tace toh Hamma kayi hakuri zan fara yin magana yanzu yace yawwa idan kina magana ma kinfi kyau, tadanyi dariya kaji Hamma da zolaya dama inada kyau ne? Yace lalle kuwa tambaya ma kike bakisan kinada kyau ba? Tace eh ni babu wanda yata6a cemin inada kyau sai yanzu. Yadanyi murmushi amma kinta6a duba madubi ai ko? Tace eh kusan kullum ina dubawa yace ai zance yakare nasan ke kanki kina yaba kanki idan kika duba madubi kamar yadda khairat takeyi, tace a'a banayi kuma ita Khairat dinma banta6a gani tana yabon kanta yayinda take duba madubi ba, yadanyi murmushi anya kuwa? Ita fa Khairat idan tayi kwalliya ni take zuwa ta fara nunawa idan nace tayi kyau sai taje ta sake idan nace batayi kyau ba sai ta barshi ahaka, Aisha tadan saki dariya meyasa take haka toh? Yace duk abinda nace yana dakyau saitace sam ba haka bane ai baiyi mata kyauba shiyasa nafada nikuma dama nasaba kushe mata ko menene, Aisha tadanyi dariya azuciyarta tace Allah sarki dan uwa akwai dadi, idan ta tuna yadda suke da 'yan uwanta duk da cewa ba uwa daba balle uba cikin nishadi suke zaman takewarsu, tana sakar Zuci Sani yace yadai ? Tadanyi ajiyar zuci sannan tace babu komai, sai yayi shiru yacigaba da tuki, yatsaya akofar wani shago yafita sannan yazagayo zai bude mata kofa saita rike tace who born me? Na isa kabudemin kofa. Yace sake mana? Tace never bazan sakeba ka kyaleni kawai nabude yasake mata kofar sannan tabude tafito tadan kallesa alamun fushi yashigesa, sai tace Hamma kayi hakuri naga kamar ranka ya6aci yadan saki murmushi iya baki sannan yace babu komai muje wannan shagon musaimiki yadin uniform , suka shiga taza6a sannan yacire kudin yabiya sun fito, tana jindadi tace hamma nago.. Yace dakata mena fadamiki dazu? Tace ah bafa godiya zanyo maka ba? Yace toh mezakicemin fadi muji? Tace dama cewa zanyi hamma namanta nagoge lambarka, yace dama kina da lambata ne? Tadanyi shiru yamika mata hannu alamar tabashi wayarta yakar6a yabincika lambobin ciki duka bawani yawane dasu ba, daga yaya Rilwan yaya awwal yaya sagir khairat zainab lauwali maishgao iya lambobin daya gani aciki kenan. Yadanyi murmushi sannan yace lalle kuwa kwana basai mota ba. Bari nasaka miki lambana din tunda kin koge, ta gyada kai alamar eh, yadubeta tareda zare idanu yadai ko bakya son lambar ne? Tace a'a inaso kasaka yasaka lambarsa sannan yadanna calling sai yaji babu kudi awayarta din sannan yace yadai bakya saka kudi awaya ne? Tace ina sakawa yakarene. Yace waye kika kira? Tace nakira su yaya Rilwan ne yadanyi murmushi hmmm sannan yadanna *663# yaduba lambarta akai ya hadda cesu sannan yasake rubuta mata lambarsa yace sai kiyi saving din lambar takar6a tayi Saving tasaka Hamma Sani akan lambar. Sannan yaja motar suka dawo har gida, tashigo tana murna tawuce har wajen Hajiya tana jin dadi ta nuna mata uniform dinta, hajiya tace ah lalle abin yayi kyau suka zauna nan sukayi ta hira da Hajiya har zuwa lokacin da khairat tadawo, adayan 6angaren kuma sagir dasafe yatashi misalin karfe bakwai da rabi yanufi gidan hhajiya fadila, kai tsaye yawuce cikin falo yasameta suka gaisa sannan yasami waje yazauna Hajiya takawo masa abinci yakarya kumallo sannan yace zanje nafara aiki Hajiya tace a'a kazauna anan muyi hira yazauna hajiya tace kazauna akan three sitters dinnan mana idan kagaji da zama saika dan mike ko yace toh yazauna suna cikin tadi hajiya tazo tazauna kusa dashi suka cigaba da tadi ahankali ahankali yalura Hajiya sai matsowa kusa dashi takeyi amma duk da haka baidamu ba. Suka cigaba da hira Hajiya tadauki wayarta sannan tasake matsowa kusa dashi tace yawwa natuna anturamin wani game amma nakasa gane kan game din tafada yayinda tacire wayarka tamatso kusa dashi jikinsu na gogeniya da juna tanuna masa game din grandthief-auto vice city, Sagir yadanyi murmushi sannan yace hajiya kenan ai wannan game din ba wahala sai yadan matsa daga inda take yaraba tsakaninsu sai tace ha'a yakuma kake matsawa, yace a'a babu komai naga kamar jikinmu yana touching ne, ah toh ai wannan ba komai bane kamatso kawai kanunamin yadda game din yake ni bazan ganeba yanda kamatsa dinnan yace haba zaki gane mana, yadan karkato da wayar yana nuna mata sai kuma tasake matsowa kusa dashi, jiyayi kamar yatashi awajen amma yalura da ita tadan makalesa haka yazauna yayita nuna mata tana cewa bata gane ba, yalura da yadda takeyi hankalinta ba'a wajen yake ba hmmm hajiya yakamata ace yanzu kingane wannan game din tadan sake matsowa tareda daura hannunta akan kafadarsa yace yadai Hajiya? Tace karka damu cigaba da nuna min kaikam hmmm akwai alamun shaidan yanaso yashiga dasauri ya ankara yatashi azabure kamar zai gudu Hajiya takama hannunsa ina zakajetafada tajawo takuma zaunar dashi, yasake tashi yatsaya yace Hajiya gaskiya kidena rikeni banaso tadan hada fuska haba Sagir dan kawai narike hannunka shine wani abu? Kai saikace badan zamani ba? Nifa babbar mata ce bawai budurwa ba kodai kanajin wani abu ne? yace wani abu kuma kamar me kenan? Tace babu komai nasan kagane ai, yadanji kamar kunya sannan yace hajiya ai ke babba ce sabida haka babu wani abinda zanji, sai tace toh dawo kazauna kacigaba da koyamin game din yace Hajiya ni gara kifadamin aikin dazanje nayi tunda nazo banyi aiki ba kawai muna zaune ga fulawowi can ba'ayimusu bayiba. Sai tace inace aikinma ai nawa zakayi ? Toh kabari nahutar dakai aikin idan kuma kana jin kunyana ne gaskiya zan baka shawara gara kadena, yace a'a hajiya banaji sai tace toh yawwa tunda ba kajin kunyata kazo kazauna yanzu ba'a kan kujerar nan ma zaka zauna ba kan cinyata zaka zauna, wani irin kadawa yaji hanjin cikinsa yayi sannan yadubeta yayinda yake faman hada gumi yace da ita.KE novels / HAKAN TAKE part 18 HAKAN TAKE part 18 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 17:06 haba Hajiya kin ko san mekike fada? Nasani mana cewa nayi kazo kazauna akan cinyata ko bazaka zauna bane? Yace gaskiya kiyi hakuri hajiya nifa bakaramin yaro bane kuma bakyau namiji yahada jiki da macenda ma muharramarsa ba. Hmmmm haba Sagir yanzu dan nace kazo kazauna shine sai ka fara yimin wa'azi ? Gaskiya kabani mamaki Sagir ko . Yace haba hajiya kinsani zama na kusa dake ba alheri bane shedan zai iya shiga tsakaninmu kuma hakan yakan iya kaimu mu aikata abinda bai dace ba, hmmm tadanyi murmushi kaga shikenan Sagir tunda bakason zama kusa dani yanzu muje na nuna maka aikin dazakayi din . Yace yawwa, suka fita tanuna masa sannan yafeshe fulawar bayan yagama yace mata zai tafi. Tace ai lokacin tafiyarka baiyi ba ko kamanta ne karfe sha biyu kuka yi kai da dan uwanka idan katafi shi kuma sai yazo? Yace eh banmanta ba naga kamar nagama aikin da kika bani dinne ai. Tace eh hakane ai koda kagama zaka zauna katayani hira . sabida ina fama da kadaici acikin wannan gidan. Yadan tsaya yana tunani , wai me matan nan take nufi dani ne? Wani zuciyar yaraya masa cewa haba yakamata kazauna kawai baidace ace kana bijirewa umarnin hajiya fadila ba. Kamar dai alokacin bashi yake sarrafa ga6o6insa ba yazo yazauna kusa da ita. Tadanyi murmushi yawwa ko kaifa? Amma gabadaya kaje kana ta gudu na kodai kyamata kake jine? Yace a'a , tace toh abinda nakeso dakai idan kazo gidan nan kasaki jikinka duk abinda nakeso kayimin kawai zan rika biyanka fiyeda yadda kake tunani. Yadanyi murmushi karki damu Hajiya yanzu komai kikace nayi zanyi miki, amma yanzu yakamata kikyaleni natafi tunda Awwal zaizo yanzu kinga karfe shadaya da rabi yanzu. Tadanyi shiru sannan tayi murmushi tace toh bakomai zaka iya tafiya idan kaje sai kace masa yazo da wuri. Yace ehen zaki ganshi insha Allahu. Sagir yatashi jiki na 6ari yace alhamdulillahi da banyi miki hakaba da bazaki kyaleni nafita ba yafada acikin ransa, kai tsaye yawuce gida. Yasami Awwal ya shirya yafito yana faman tafiya gidan hajiya. Yadan kallesa taab dan kwalisa kasha wanka. Amma fa sai dai ince Allah yakiyaye ka. Awwal yadubesa sannan yace menene zai faru dani har kake cewa Allah yakiyaye? Yadanyi murmushi kaikam zakazo kabani labari kayi sauri kaje yanzu hajiya tana jiranka. awwal bai tsaya ko ina ba yawuce kai tsaye. A6angaren Rilwan kuma shida Sadauki suna nan suna harkar yahoo yanzu ya fahimci abubuwa dayawa kusan ya fara zama kwararre aharkar. Idan yazauna yashirya salon damfarar mutane ayanar gizo sadauki shi kanshi abin mamaki yake bashi, Bayan Sadauki ya tabbatar da Rilwan yagane harkar sai yake sanar masa cewa zaiyi tafiya zaije london idan kuma yaje zaiyi wata 6 sabida haka acikin watanni shidannan inaso yakasance kayi kokari kaima kayi abin kanka acikin wannan harkar. Rilwan yace karka damu zan baka mamaki oga kafin kadawo zaka ga abubuwan da zanyi. Hmmm lalle kuwa zangani idan kayi maikyau ma kanka kayiwa, Rilwan yace babu komai oga yaushe zaka tafi sadauki yace gobe nakeso intafi sannan yau kuma akwai wani birthday din wata friend dina data gayyaceni inaso muje dakai wajen sabida akwai 'yan yahoo dayawa idan mukaje zan nuna makasu amma karka yi yadda zasu fahimci cewa kaima dan yahoo ne. Rilwan yace toh bakomai. sadauki yace toh yanzu kaje kashirya kadawo bayan sallar isha sai mutafi. Rilwan yace toh. Bayan Awwal ya iso gidan Hajiya fadila yayi sallama yaji shiru kai tsaye yashige cikin falo yana sallama amma duk da haka shiru alokacin sai yayi tunanin ko tashiga toilet ne sabida haka sai yasami kujera yazauna yana zama yaji wayarsa tafara ringing yaduba lambar Hajiya ne yadauka tareda sallama sai yaji tana cewa ina cikin daki ka kariso. Yace lafiya kuwa tace a'a ba lafiya ba ciki na ne yake ciwo. awwal yace subhanallahi yakashe wayar sannan yanufi dakinta cikin hanzari. Yabude kofar sannan ya yaye labulen, wani irin faduwar gaba yaji yayinda ya kalli Hajiya cikin dressing din dayayi matukar tayar masa da hankali. Daga ita sai singleti wanda shima ko cibiyarta bai isoba sai kuma gajren wando wanda ko cinyarta bai gama rufewa ba. Yajuya tareda kawarda idanunsa , I am sorry Hajiya banyi tsammanin zansameki undressed ba kiyi hakuri dan Allah, yafada yana faman fita idanunsa na kallon gefe, tace Awwal ina zakaje kuma while i told you that bani da lafiya kasani bazan zauna haka ba matukar lafiya na kalau ba wai son raina bane kataimaka ko agajin gaggawa ai yakamata kamin. Jin tafadi haka yasa yajuya jikinsa asanyaye yaje yabude wardrop dinta yaciro wani zani yazo yadagata ahankali yalullubeta dashi tadafeshi ajikinta yace toh Hajiya kin rikeni dakarfe kuma kinada nauyi sosai bazan iya dagaki nikadai ba bari nakirawo ko mai gadi ne yazo yatayani mukaiki asibiti, tace no just kyaleshi kawai ka kokarta yasaka hannu yadagota sai yaji ta wantsalashi ta harbashi tabaya sannan tanufi kofar dakin takulle tarike keydin ahannunta, ahankali yatashi yana mamaki. Hmmm wane irin sharri Hajiya takullamin ne? Yatambayi kansa yarasa amsa yadaga kai yakalleta yayinda takuma cire zanin da ya lullu6eta dashi ta ajiye agefe, sannan tace ina fatan kafahimci abinda nake nufi ko? Take zufa ta malale ajikinsa zan fahimta dai hajiya yafada, uhmmm zo na fahimtar dakai tana matsowa kusa dashi yana ja da baya, hmmm Hajiya babbar macece mai jiki gata da karfi matukar ta damke sa ya tabbata bazai iya kufcewa ba. Tace meyasa kake ja da baya katsaya mana haba Awwal inaso muyi maganar fahimtar juna dakai kayi hakuri kabani kanka na wannan lokacin, nayi maka alkawari zan baka duk abinda kake so ko naira nawa ne kafada zan baka. Yace Hajiya kiyi hakuri wannan abin bakyau tace haba Awwal nasani ba kyau amma abubuwa marasa kyau nawa ka aikata kuma kake kan aikatawa ina rokonka kataimaka nasan dan uwanka yafada maka yadda mukayi dashi kuma kazo ina fatan kai zaka bani hadin kai fiyeda shi kaji. Yadanyi shiru yana nazari sannan yatuna maganar da Sagir yake fada masa yayin da yadawo. Dan kwalisa wannan wankar taka tayi amma fa saidai ince Allah yakiyaye, babu komai duk abinda yafaru zakazo kabani labari, zantukan da suka fara kaiwa da kawowa kenan acikin kwanyarsa kenan Sagir ni zaiyiwa haka? yasan abinda zai faru dani kuma bai fadamin na shiryama abinba. Kafin ya ankara ji yayi taciro wani garin powder ta hura masa batareda yasani ba yasheka alokacin yaji karfin jikinsa gabadaya yagushe tsayawa ba da kyar ya tsaya akan kafafunsa yana tangal tangal, Isowa jikinsa da tayi takamashi tawurgashi kangado suka fara kokuwa kasancewar tafisa karfi hakan yasa tabankarashi sosai tayaga masa riga tacire tawurgar da rigar agefe tun yana dafewa har abin ya faskara daga karshe saida tasamu tabiya bukatarta sannan tasakesa yatashi yana kuka ni kikayiwa fyade Hajiya? Wallahi zakiyi nadamar abinda kikayimin wallahi sai na yimiki abinda bazaki ta6a mantawa ba har karshen rayuwarki. Tace kayi hakuri Awwal wallahi babu yanda na iya ne amma tunda yanzu munfara dan Allah kayi hakuri kazama partner dina juyawa yayi yacika mata fuska dayatsu ke bakida hankali ne . Tunda nake banta6a sanin wani abu makamancin wannan ba , and you have disvirgined me today and you wil see the pay back of what you did to me yafada sannan yanufi kofa yana kuka zai fita sai kuma yaga kofar akulle yatsaya yajuyo kizo kibudemin kofa, tace ok tataso ahankali tabude masa kofa tana murmushi yace zakiga abinda zanyi miki. Kai tsaye yafito farfajiyar gidan sannan yanufi famfo yaje yawanke jikinsa sannan yaje yasami maigadi yakar6i rigarsa yasaka sannan yanufi gida zuciyarsa na tafa. Yana zuwa yasami sagir akwance acikin daki ko sallama baiyiba ya damkesa yadagosa ya sauke mari . sagir yatashi Awwal lafiya kuwa kake marina mutumin banza maci amana, Awwal yafada yayinda yakara kaimasa duka yasamesa akumatu alokacin bakin Sagir yafashe Awwal yaturashi yahadashi da jikin bango, dakai za'a hada baki acutar dani Sagir haba habba sagir kabani mamaki awwal yana magana idanunsa kamar zasu fito, sagir yace mehakanne kam wai meyafarune kazo sai duka na kakeyi, bansani ba ai kafi kowa Sanin abinda kayi min Awwal yakuma daga hannu yakaima Sagir duka sai yarike hannun suka kama ko kuwa Sagir yana ce kasaurara mana wai me hakane kam Awwal sai bugu yake kaiwa Sagir yaga abin bamai yiwuwa bane kawai shima sai yafara kaima Awwal duka nan suka kaure fada ta rinca6e tsakaninsu, sai ga Rilwan yadawo kamar anturo da sako, kai mehaka me kukeyi haka? Yazo yashiga tsakaninsu you are very stupid da girmanku zaku zauna kuna yin fada akanme? Mehaka ko sauraronsa Awwal baiyiba yasake kaima sagir bugu Rilwan ya rikesa sannan yaturesa gefe. Wai mehaka ne Awwal me yashiga tsakaninku aduniyar nan da dayanku bazai iya hakura yasaudakar ma dan uwansa ba har sai kunyi fada akai. awwwal kuka yakufce masa yayinda yatsaya yunkurin fadama Rilwan abinda yafaru tsakaninsu. Rilwan yakalli Sagir wai me yafaru tsakaninku ne? Sagir yace nima bansani ba ina kwance kawai yashigo yahau kaina da duka. Awwal yace karya kake makaryaci kasan abinda kashirya min. Rilwan yace dakata Awwal cool down kayi hakuri menene yashirya maka.? Awwal yace mutumin banza ne dashi aka hada baki aka keta min mutunci, kamanya aka keta maka mutunci Rilwan yatambaya, Awwal ya kwashe duk labarin abinda yafaru tsakaninsa da Hajiya yasanarma Rilwan alokacin yaji Sagir yafara salati. Wallahi nima hakan taso tafaru dani da naso nasanar maka amma sai na sha'afa. Wallahi Hajiya mutumiyar Banza ce fiyeda tunanin jama'a kai rufemin baki munafuki inace hada baki kukayi dakai tacuceni nasani kabata kanka tabiya bukatarta da kai. sagir yace wallahi tallahi ni bataci nasara akaina ba kuma ko kur'ani zan iya rantsewa akan hakan. Rilwan yace toh ya isa please yakamata muyi maganar fahimtar juna . Yanzu kowannenku yayi mana bayani daga farko har karshe abinda yafaru tsakaninsa da ita. sagir ya kwashe bayani kaf yazantar musu Awwal ma yakwashe bayaninsa kaf yazantar. Rilwan yayi ajiyar zuci haba Awwal ai kayi saurin yanke hukunci. Shin ita hajiyar wannne irin hukunci kadauka akanta da har zakazo ka kama dan uwanka da fada haka? Meyasa kayi saurin yanke hukunci haka? Ai ba Sagir ne yadace kadauki mataki akansa ba ita Hajiyar ce yakamata kadauki mataki akanta, wani irin mataki zan iya dauka akanta? Matanda tariga tafini karfi nesa ba kusa ba. Hmmmm gaskiya toh abinda kayi baidace ba kaduba kaga har fasa ma Sagir baki kayi ni abin yayi matuka bani mamaki, tun muna kanana banta6a ganin kuna fada ba sai yau yau dinma sabida sharrin wata mace. Mace mace mace itace dake so tayi destroying na Relationship din dake tsakaninku harma dani baki daya toh karya take idan tanayiwa wasu mazajen haka tana kwana lafiya toh wallahi yau ta ta6o abinda zatayi nadamarsa koma wacece ita idan bazaku dauki mataki akanta ba ni zan dauka laifin fyade bakaramin laifi bane we must go and take a revenge Rilwan yafada yayinda idanunsa sukayi jaaa suka kada shi babu abi mafi muni da kuma tada masa hankali kamar ganin 'yan uwansa suna fada iska dayayi sabida sharrinta,AKE part 19 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 17:08 Rilwan yadan tsaya yarike kunkumi yana tunani sannan yayi ajiyar zuci ,dole ne mudauki mataki akan wannan matar , hmmm wanne irin mataki kenan kake gani zamu dauka akanta wannan matar kudi ne da ita sosai gata kuma da karfi babu yanda muka iya da ita, Awwal yafada cikin juriya, kana nufin mukyale ta kenan? Iyeh? Tambayarka nake Rilwan yakaraso inda yake yana zance afusace, babu yadda za'ayi mukyale wannan matar. Kai ko kun kyaleta ni bazan kyaleta ba, dan banta6a jiba inda akace yau gashi mace tayiwa namiji fyade, sai akankaa. Gashi kuma wai har kana faman cewa babu yadda muka iya da ita. Ita waye wacece ita? She is nothiong but useless. Wallahi ko kun hakura ni ban hakura dole ne naje na... Alokacin yaji wayarsa tana ringing yadauka yaga Sadauki ne sannan yakara akunnensa hello oga . Sadauki yace lafiya lau ya dai nashirya kai har yanzu baka dawo ba kai nake jira fa? Kazo mutafi. Wajen bikin birthday dinnan Rilwan yace ok oga ina zuwa nadan tsaya wani aiki ne kadan. Sadauki yace ok kar kajima dan Allah. Rilwan yace bamatsala oga. Sannan yakashe wayar Rilwan yace oga na yakirani zamuje bikin birthday din wata friend dinsa so please dan Allah abinda nakeso daku musamman kai Awwal yakamata ka tsaya kafahimci abu kafin kace zaka dauki hukunci akai. Kaga yanzu kaji masa ciwo haka kuma kaga bashida amfani please kadena ita Hajiyar taku nasan irin hukuncin da zan dauka akanta. Rilwan yawuce ciki sannan yayi dressing yafito, yasamesu suna hirar Hajiya abin yaso yabashi dariya amma ahaka sai yadaure sannan yace ni natafi sai anjima suka amsa toh sannnan yafita kai tsaye yawuce gidan Sadauki. Yaje yasami Sadauki yashirya suka shiga motar Sadauki basu tsaya ko inaba sai Night club suka shigo akaje aka tarbesu cikin karramawa hakan yasa Rilwan yafahimci cewa tabbas awajen suna girmama Sadauki. Aka kaisu inda zasu zauna sannan aka sake wata sauti waje ya rinca6e sai rawa kawai akeyi. Abinda Rilwan baita6a gani ba amma aranar yakalla. Aka kira Sadauki cikin fili shima yashiga sukayi rawa shida wata abin sai yabawa Rilwan dariya. Yakasa daurewa yarike dariyan musamman salon rawar sadauki gabadaya dariya take bashi. Aka kwashe nishadi sosai har misalin karfe daya da rabi cikin dare Sadauki yace ma Rilwan zamu tafi ko? Rilwan yaduba time sai yakalli karfe 1:35am yace kuut oga ni bansani ba ashe mun kusan kwana anan wajen.? Sdauki yace meyasa kafadi haka. Rilwan yanuna masa agogon dake hannunsa sadauki yakalla sannnan ya tashi yaje wajen wacce tashirya bikin yasanr mata cewa sukam zasu tafi tayi masa godiya sannan suka tashi suka rako Su Sadauki bakin harabar club din suka shiga motarsu suka barwajen. sadauki yajuya yakalli Rilwan anya kuwa kata6a zuwa wajen chasu? A'a wallahi banta6a zuwa ba. Yabashi amsa hmm lalle kuwa naga alama ai sai kallon 'yan mata akeyi. Rilwan yadanyi murmushi wallahi gidan akwai dadi gobe ma zamuzo ko? Sadauki yakyalkyale da dariya hmmm dan banza babu zuwan da zamuyi ko kamanta ne gobe zayi tafiya? Rilwan yadanyi ajiyar zuci eh hakane natuna yafada sannan sadauki yace ai nan wajen dakake gani kullum sai anyi chasu anan, yanzu ne ma na rage zuwa amma da kullum ina can, hmmmm oga kace ka dane kana shanawa, yadanyi murmushi hhhhh ai abin jaraba ne yanzu Allah ya ragemin son abin sosai. Har zuwa mazaunin Rilwan yakawosa sukayi bankwana sai dasafe sadauki yace zamuyi waya. Rilwan yashiga kai tsaye yasamu su Awwal duk sunyi bacci, nan shima yakwanta taje bacci yayi awon gaba dashi kasantuwar gajiya dake mamaye da dukkan jikinsa. abangaren Aisha kuma tafara zuwa makaranta sai kokari takeyi abubuwa dayawa sun sauya mata kullum takan kai ziyara ga 'yan uwanta dake gidan lauwali maishago. Hakan yasa Sani yamatsa cewa yakamata amatso dayaran kusa da ita. Sabida haka Sani yasami Lauwali maishago yayi masa zancen. Lauwali yace sam bazai yiwu ba Fatima da Bilal sun zama yaransa sabida haka bazai iya rabuwa dasu ba. Acewarsa sunyi sa'a ma da ya yadda yabar musu Aisha awajensu babu yanda Sani baiyi ba amma lauwali maishago yaki , haka Sani yahakura taci gaba da yadda takeyi din. Akullum mamaki baya gajiya da ziyartarta kasantuwar yadda Sani yake tarairayar ta har ta fahimci cewa tsakanin biyu akwai daya ko kuma akwai duka biyun. Nafarko soyayya. Nabiyu ko kauna. Wannan shine abinda takasa tantancewa, akullum idan suka zauna suna hira da khairat sai ta kawo mata zancen Aisha shin har yau Hamma Sani bai furta miki cewa yana sonki ba? Murmushi kawai tasaka sannan tace kawata kenan. Wai waye yace miki Hamma sona yake? Ni ina ga kamar yadaukenice amatsayin kanwarsa yakan yimin duk abinda nakeso sannan yana nunamin kauna. Khairat tayi murmushi sannan tadubeta Aisha inaso nayimiki wata tambaya shin ko zaki iya yin soyayya da hamma? Aisha tadanyi shiru tana nazarin tambayar sannan tadubeta cikin alamar wasa tace bangane ba? Cewa kikayi zakimin tambaya shin ai ban baki izinin yimin tambayar ba. Hmmm nidai amsa kawai na bukata khairat tafada yayinda take faman cijewa. Saida taja wata doguwar ajiyar zuci sannan tace khairat tunba yauba na fahimceki duk take takenki so kike kihada soyayya tsakanina da Hamma Sani, toh amma kuma abinda bakiyi tunani akai ba shine kinfasani kuma nasha baki labari cewa ni banta6a soyayya da wani da namiji ba. Kamar yadda kema kike furtamin hakan. Nasani babu yanda za'ayi ace namiji kamar Hamma ba a sami wata mace wacce zata kai masa tayin soyayyarta ba, kodai shi yakaimata tayin soyayyarsa ba. Idan kikayi bincike zaki samu akwai wacce take zuciyarsa kinga kenan zai iya yiwuwa na fada cikin sonsa shikuma yakasance bani yakeso ba. Murmushii khairat tayi sannan tace idan Hamma na ne karki damu kedai abinda nakeso naji daga bakinki shin idan yafurta miki cewa yana sonki wace irin amsa zaki bashi. Shiru Aisha takuma yi akaruna biyu daga bisani tace wato azahirn gaskiya Khairat bazan iya fuskantar mutum kamar hamma Sani ince masa bana sonsa ba musamman irin mutunci dakuma alherin dayayi min bazai yiwu yakawo min tayin soyayyarsa naki amsa ba. Khairat tace Good abinda nakeson ji kenan. Sabida haka zakisha mamaki yanda zan hada soyayya atsakaninku. Aisha tayi murmushi toh ayi dai mugani. Khairat tace lalle kuwa kina wasa da al'amarina za'ayin kuma zakuganin . Takuma saka murmushi sannan tace toh Allah yanuna mana. A6angarensu Rilwan kuma washe gari dasafe bayan sallar asuba Suka zauna suna tadi acikin dakinsu, Awwal dai shiru baya iya yin zance Rilwan yadubesa Awwal yadai? Lafiya kuwa? Yana dago kansa Rilwan yaga hawaye sharkaf acikin idanunsa. Yadai tun abin jiyanne haryanzu baka huce ba? Da hanzari yatashi cikin sheshshekar murya yake zance tayaya za'ayi inhuce? wallahi bazan kyaleta ba dan zancen gaskiya yanzu haka yacancanci nadauki hukunci akan wannan matar wallahi. Riilwan yace karka damu ka kwantar da hankalinka komai cikin Nitsuwa akeyi, kaga ita wannan zamanin da muke ciki idan baka iya kama 6arawo ba shi zai kamaka. Inaga lokaci yayi daya dace ace muma munfara aiwatar da duk abinda zamuyi cikin tsari da kuma nitsuwa, wanda rashinsu ne yasa mukayita faduwa abaya, awannan zamanin da ake ciki, anayin amfani ne da abubuwan da zamani yake tafiya dasu wajen kama mai laifi ko kuma daukan fansa bisa abinda akayi maka,, sagir yace nifa ban fahimci inda kadosa ba. Rilwan yace karka damu zaka fahimta. Abinda nakeso yanzu haka daku , so nake ku koma gidan hajiya fadila kusato min abu 2 idan kuma akwai na ukun to dai ku hada yazama na 3. Awwal yace menene kakeso musato maka?. Sonake kudaukomin wayarta. Dakuma Atm dinta sai kuma computer idan tana dashi. Inaga batada computer wayai ne kawai. , Rilwan yace toh tunda batada computer abune mai sauki kawai wayanta da kuma atm dinta nake bukata. Sagir yace angama amma wai waye ne zai fara zuwa satar. Rilwan yace, kai ne zakake. Idan sai kayi kokari kasace mata waya first. Nabiyu sai kadauke atm card dinta ina fatan kasan irin hanyoyin dasuka dace,sannan kuma idan kaje kasaki jiki da ita kar kanuma mata cewa abinda yafaru jiya tsakaninta da Awwal kasani. Kawai kanuna mata cewa babu abinda kagani na tsana game da ita, daga nan nasani zatayi tunanin ko kunya yahana Awwal furta ma Sagir abinda yafaru tsakaninsu. Haka zakayi ta lalla6ata dekyau har zuwa lokacin da zakayi nasaran satar wannnan abin kuma karya wuce yau zuwa gobe. Awwal yace amma wane irin mataki ne kuma wannan tahanyar sace mata waya da kuma Atm. Rilwan zaiyi magana sai yaji wayarsa tafara ringin ahankali yadauka yaga sunan Sadauki ya bayyana afuskar wayarsa, hello oga yadauka yayinda ya katse hirar dayakeyi din. Sadauki yace inaso kazo yanzu sabida nakusan tafiya jirgin nan zata tafi kuma kasan idan wannan jirgin tatashi zaiyi wuya nasamu wata. Rilwan yace toh gani nan zuwa yafada. Sannan yatashi yafara shiryawa yace zanje wajen oga na yanzu haka yanaso zaitafi kasar india sabida haka bari naje muyi bankwana dashi idan kaje gidanta sai kayi kokari kayi abinda nace. Sagir ya amsa toh. Rilwan yafito alokacon da sanyin safiya sosai. Yatari dan aca6a yakaishi har kofar gidan sadauki sannan yashiga yasamesa yagama shiryawa. Shigowarsa yace yawwa daman kai nake jira. Yadauko computer dinsa yamikawa Rilwan yace kayi amfani da wannan computer din wajen aiwatar da wannan harkar din har zuwa kaima kasayi naka. Amma kafin nadawo watanni 6 katabbata cewa kasayi naka computer din. Rilwan yayi godiya sannan yace oga babu damuwa zanyi duk abinda kace. Sannan kuma idan akwai Hali kazo kuzauna tareda sauran gayuna kurika kwana taredasu mana? Rilwan yace uhm oga kenan kaikam dai sai ka dawo Allah yakiyaye hanya.. Yace ameeen Rilwan yarakasa suka tafi Har airport . Suka tashi Rilwan yadawo gida da computer dinsa. Yana nan sai yafara tuna harka kawai. Saidai abin bazai tafi maikyau ba, sabida akodayaushe sadauki yana kara masa guideliness akan abin yanzu kuma gashi sadaukin yatafi. Sagir aranar yaje gidan Hajiya dasafe yana zuwa yagaisheta cikin karramawa sannan ta amsa alokacin tambayar data fara yimasa kenan yaa Awwal yana lafiya? sagir yace lafiya lau. Tadany ajiyarr zuci sannan tace toh madallah. Tazo kusada Sani yauma taciro wayarta tamika masa sannan tace still daman jiya bankoya ba sabida haka yaukam sai ka koyamin. Yadanyi murmushi sannan yakarbi wayar yayi irin zaman datakeso yazauna yake nuna ba. Ita kanta abin yabata mamaki. Sai take sakawa cewa ai sagir yafi Awwal wayewa duba fa yadda mukayita kokowa dashi ma. Uhm ahakanma nayi amfani da powder hmmm da wannan natsaya ai da babu ruwana. Katseta yayi da zancen yayinda yake nuna mata kuma yashiga game din. Ta tashi Sagir bari nakawo maka fruit kasha ko? Yace ok hajiya hajiya tashiga wani bangare sai kawai Sagir yatashi yashiga dakinta kai tsaye yafara yimata bincike aikuwa cikin sa'a yana bude drower dinta yakalli AtM dinta na First bank dasauri yadauka sannan yasaka Aljihu yafito yazauna afalon sai ga takawo masa fruit din yadauko zaisha sai yatuna wani abu sai kuma yatuna wani abu sai kuma yafasa, yatashi bari na da fita nan, tace ina zakaje kuma muna zaune muna hira. Yace badamuwa Hajiya gani nan ai batafiya nayi ba tunda ga nan wayarki ma ahannuna, toh bakasha ruwan lemun ba, yace eh nasani Hajiya ina zuwa. Yafita kamar da wasa tajira bai dawoba tafito tabincika samada kasa baya nan tafito ta tambayi mai gadi yace mata ai yatafi, tasami wani waya takira yashiga akadauka. Hello tafada sannan tace ina kashi gane Sagir? Ba Sagir bane Awwal ne . Tadanyi turus sannan tace toh Awwal lafiya kuwa kuka daukamin waya? Har kina da bakin tambaya lafiya ko ba lafiya ba? Shin kina nufin kinmanta abinda kikayimin jiya ne? Adaidai lokacins saiga Rilwan yashigo yasami Awwal yana waya da ita bayan yagama sannnan yace mukalli wayar? Yamikawa Rilwan yakalla sannan yace hmmm dakyau bari nadanyi mata bincike kadan, Rilwan yakar6i wayar yabude shafin whatsAp subhanallahi abinda yafada babu abinda yaketa gani face hotunan batsa dauka video din batsa. Haka kuma dun wani chat idan yabude sai yaga batsa ne. Yanuna musu komai sannan yace . Bari yagwada hawa facebook yagani yashiga yabude babu abinda yake ta gani face sugar mummy sugar mummy. Ajiyr zuciyayi sannan yace ,KE novels / HAKAN TAKE part 20 HAKAN TAKE part 20 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 17:10 dama nasan za'a rina wannan matar fa sugar mummy ce.. Me kuma sugar mummy sagir yatambaya? Hmm bakasan Sugar Mummy ba? Duk rike wayarka da hawa social network dinka? Sagir yace da ace nasani da zan tambayeka ne? Hakane sugar Mummy wasu mata ne ko kuma ince karuwai manya kuma masu arziki ne aikinsu dai shine su Sami saurayin matashi yarika biya musu bukata sukuma su rika biyanshi kudi. Awwal yace zamani kenan idan kana da rai babu abinda bazaka gani ba . Hmmm yanzu ba wannan ba me abinyi Sagir yatambaya. Yanzu kam abinyi shine zamuje banki muyashe duk kudin dake cikin asusunta, tunda ga ATM dinta ahannunmu sannan kuma ga wayarta nan. Kagani bazata gane cewa muna diban kudinta ba sai mungama sai mu maida mata wayarta. awwal yace eh toh muyi hakan amma fa duk abinda zamu diba kasan bamu isa mu talautar da matannan ba, sabida tana da arziki fiyeda yadda muke zato. Karka damu da arzikinta kawai diyyan fyaden da tayi maka ne zamu cire idan muka gama sai mu maida mata atm dinta. Toh ba matsala Sagir yafada sannan yace yaushe kenan zamu fara cire kudin? Rilwan yace yau mana ayau zamuje mucire. Kunema zakuje nikam akwai inda zanje sabida haka idan kunje ma sai dayanku yabude mana sabon account idan kun cire kudin daga can sai kuyi mana deposit kawai. Suka amsa toh. sagir yace gaskiya Rilwan yanzu har mamaki kake bani? Rilwan mamaki kuma name? Yadda kake ta sarrafa kwakwalwarka wajen shirya sata mana gaskiya zamanka da sadauki dinnan yakara maka experience, yadanyi murmushi aikuma yanzu zaku zama yahoo boys tunda muna tare oga na yayi tafiya sabida haka komai ahannuna yake, toh bamatsala. Su Sani suka shirya suka tafi first bank sukayi duk abinda Rilwan yace suyi sannann suka dawo alokacin basu sami Rilwan agida ba. Yatafi gidan sadauki yaje yayi amfani da wifi dinsa yayi wasu ayyuka sannan. Yafita bai tsaya ko ina ba sai club duk dacewa alokacin da rana ne amma akwai mutane awajen kasantuwar wajen akwai masu sayarda abinci dasauransu. Rilwan yaje yasami waje yazauna yace akawo masa abinci alokacin sai yafito da wayarsa yafara latse latse. Saiga wani yazo cikin maye yana tangadi yana tafiya hannunsa rikeda kwalbar giya. Yazo yazauna kusa da Rilwan kai yaro kazo shakatawarka ne kaima? Rilwan yadan kallesa yana dariya shayayye kawai ni fa bana son matsala. Yakara matsaowa yace ai idan matsace kahadu da ita yau. Ya sunanka yatambayi Rilwan kai me damuwanka dasuna na? Rilwan yamaida masa martani. Hmmm yadan jaaa murya yayinda giya ta dusar masa da muryarsa uhm antambayeka din me sunanka ? Bazan fadaba Rilwan yabashi amsa sannan ya tashi yabar wajen yakoma wani waje shikuma saurayin sai yagyara zamansa dai dai inda Rilwan yazauna sannan yafitar da wayarsa shima yana dan dannawa alokacin da ma aikaciyar abincin ta kawo ma Rilwan abincinsa kai tsaye tawuce wajen wanda yake mayen takai masa ta ajiya masa batareda ta lura da cewa bashi ne yace akawo masa abinci ba.. Ta ajiyase tareda durkusa kadan shiko yakar6i abincin yafara ci tajuya tana tafiya Rilwan yafara kiranta ke yadai tun yaushe nazo ne kin manta dani kinje kin bawa wannan shayayyen? Tajuya takallesa oh my God wallahi nazata cewa kaine acan wajen shiyasa nakai masa kayi hakuri bari naje nakawo maka naka kayi hakuri dan Allah. Ok bakomai yafada sannan. Tawuce yabita da harara aransa yace wai wancan shayayyen tayima kallo na? Hmm wannan itama bata gaza hakan ba, takawo masa abinci yazauna yaci sannan yatashi zai tafi mashayin yabiyo bayanshi abokina tsaya mana muyi magana. Rilwan ya waigo yakallesa kai waye abokinka din? Yace kai mana bagashi kasayamin abinci ba? Waye yasaya maka abinci kaide kasayawa kanka. Rilwan yajuya zai tafi yarike rigarsa Rilwan ya hankadesa yawuce mai kar6an kudin abinci yamikawa Rilwan bill na kudin abincin da aka kai musu harda mashayin nan . Rilwan dafarko yayi kamar bazai biya ba , daga bisani kuma yacire kudin yabayar sannan yafi yafara tafiya shayayyen yabisa yakuma tare gabansa wai kai meyasa bazaka saurareni bane? Inada kudi fa karka ganni haka karaina min hankali yana magana kamar an shakesa. Rilwan ji yayi ya tuntsire da dariya sannan yace masa toh naji yi hakuri mekudi na ji zan saurareka mekakeson fadamin. Yace goood haka nakeso ai amma kai gabadaya kabi ka hadamin fuska sai kace wani abokin gaban ka?.. Ni fa zantafi idan bazaka fadamin abinda kayi niya ba. Toh tunda kana sauri bari kawai infada maka suunana sabida idan munhadu nangaba sai ka kirani kaji? Rilwan yagyada kai alamar eh , Sunana Uzairu sabida haka kayi kokari ka hadda ce wannan sunan kamar karatu, Rilwan yace hmmm naji zan haddace yafada yana dariya sannan yacemasa sai anjima ko? Mashayin yace yawwa kagaida mamanka. Rilwan yace toh. Suka rabu mashayin yakama hanyarsa Rilwan ma yayi gida. Yaje yasamesu Sagir adaki kai tsaye yahaye gado sannnan yace musu me bayani sukace komai normal, yace good abin yayi kyau sosai. Gobe nakeso mumaida mata kayakinta wayarta da ATM dinta. Awwal yace sabida me zamu maida mata. Yace sabida akwai abubuwa masu muhimmanci da take amfani dasu awayarta idan muka raba ta dashi mun cuceta sosai sabida haka inaga abinda yafi dacewa dai shine zamu mayar mata amma fa bazamu kyaleta ba zamuyi mata dankaren duka wanda ko sunanmu taji zataji kamar za'a saukar mata azaba. Hmmm taya kenan kake ganin zamu dauki irin wannan matakin? Rilwan yace zaka gani idan munje. Toh bamatsala suka ce toh shikenan za mugani din. Dare misalin karfe takwas Rilwan yayi wanka yatafi club. Yasamu anayi kamar najiya yasami waje yazauna. Yana dan latse latsen waya sai ga kira tashigo masa dubawar dazaiyi sai yaga lambar kasar india hakan ne yatabbatar masa cewa sadauki ne , hello oga yafada yayinda ya kara wayar agefen kunnensa, hi yane Rilwan Allah yayi isowa na fa? Yace toh oga ya mutanen india din? Sadauki yadanyi murmushi hmmmm gasunan dai 'yan mata sai safa da marwa suke a area din danake. Hhhh oga kabi ahankali dai kar kaje 'yan mata suhanaka yin abinda kajeyi, haba saikace wani sakarai, ko zan kulasu bazasu hanani komai ba, Rilwan yace toh nidai haka nake fata, Sadauki yace toh yanakejin kida natashi akusa dakai ? Rilwan yace eh nazo club din damuka je dakai din nan ne, hmmm shikenan kaima kafara kenan Allah ya sa kadena Rilwan yace toh nidai bana aikata komai amma bazanki cewa Ameeen ba, ehen toh ya batun harka, Rilwan yace eh ina gudanarwa amma oga wallahi idan babu kai abin ba dadi, hmmm karka damu 6 months kawai zanyi kaide kacigaba da kokari kasamu kahada kayan aiki naka kaima, toh oga zanyi iya bakin kokari na yace yawwa sai mun sake yin waya, Rilwan yakashe wayar waigawar dazaiyi sai yaga wancan mashayin agefensa yayi wanka yaci gaye bisa dukkan alamu yanzu baya cikin maye, yamiko ma Rilwan hannu suka gaisa yace masa sannu ko abokina dazu ina cikin maye ka sayamin abinci nagode fa amma kaki fadamin sunanka ? yadanyi murmushi Sunana Rilwan , kacemin sunanka uzairu ko? Yace eh uzairu amma ko UZi boy kafada yayi, Rilwan yace dakyau Uzi boy gaka handsome guy amma kana shaye shaye why? Uzairu yadanyi murmushi hmm karka damu ni abinda nakesha ba wanda zai cutar dani bane, kamanya ba wanda zai cutar dakai ba giya din ne bazai cutar dakai ba kome? Uzairu yace eh iyakaci na idan nasha nakwanta nayi bacci nahuta idan natashi shikenan sai naji jikina fresh, Rilwan yadan saki dariya amma dazu baka ga yanda kakeyi bane shiyasa dan kuwa yanda kake tafiya mota zata iya bugeka idan kuma akayi haka toh kagani kenan kasha abinda zai cutar dakai. Toh ni inba yau bama banta6a shayuwa nakama hanya ba, yau dinma sabida kai ne. ni idan nashayu kwanciya nakeyi sai nadawo hayyaci na kafin nakama hanya. Kuma ni bana shan hayaki balle ya6ata min kayan ciki. Ko baka shan hayaki amma kana shan abinda zai bugar dakai ai? Eh dama buguwan nakeso ai. Haka sukayita zance alokacin har suka fahimci juna, can dare yayi misalin karfe 11 Rilwan yatashi yace Uzi boy ni zan tafi sai yace tsaya mutafi tare. Suka fito harabar gidan kai tsaye yaje yabude wata mota 307 Rilwan yazuro masa idanu yace zo mu tafi mana? Kutt ashe dama wannan shayayyen yana da kudi har haka? Rilwan cike damamaki yaje yashiga suka fara tafiya Rilwan yace abokina wannan motar kace? Yace eh mota tace? Kai amma kai dan mekudi ne ko? Uziboy ya tuntsire da dariya ni ba dan kowa bane wannana motar da kudi na nasaya asali ma ba'a gidanmu nake ba yanzu, toh awane gida kake yace agidana nake zaune nida yaron gidana, dakyau muje a camp loveth hotel zaka ajiyeni, yace toh suka iso wajen Uzairu yafaka sannan suka sauka yace muje site dinka ingani suka shiga alokacin Awwal da sagir sunyi bacci. Uzi boy yace wadannan fa? Rilwan yace 'yan uwana ne . Wai kana nufin ahotel kuke da zama dindindin? Eh wallahi zuwanmu garin nan kusan watanni 2 kenan anan muke. Uzi boy yace bamatsala kawai kutattare kudawo gidana akwai dakuna dayawa wadanda babu mutane aciki. Rilwan yace hmm kana ga ahakan babu matsala? Yace me matsalar gidana ne fa? Ko dayake gobe zanzo insameka anan zamuje kaga gidan Rilwan yace ok bamatsala Uzi yakama hanya zai tafi Rilwan yace jimana Uziboy,, yadan waywaya yakallesa, namanta bantambayeka ba menene sana'arka? Yadanyi murmushi sannnan yace sana'ata kawai sarrafa Na'ura mai kwalkwalwa ce kawai. Rilwan yadanyi murmushi kamar dai sana'armu tana kama, mene taka sana'ar Uzairu yajuyo yakuma tambayarsa, ni dan yahoo boy ne, uzairu yadan saki murmushi dan bala'i kace Kawai Allah ne yahada mu kawai sabida muyi harka tare, uhm Uziboy ya maka turanci; I had hacked into a lot of companies, and took copies of the source code to analyze it for security bugs. If I could locate security bugs, I could become better at hacking into their systems. It was all towards becoming a better hacker. Yamika masa hannu suka tafa.. There are a thousand hacking at the branches of evil to one who is striking at the root. Suka kuma tafawa suna shewa tareda zance dakarfi acikin dakin hakan yasa su awwal farkawa daga bacci, sagir yatashi kai su wane ne? Yafarka da sauri yakallesu Mtswww kunzo kunbi kuna damun mutane karfe shabiyu da wani abu fa? uzairu yace toh bari natafi kaikam sai da safe zamu sake tattaunawa dakai. Rilwan yace toh bamatsa hakan takeAKE novels / HAKAN TAKE part 21 HAKAN TAKE part 21 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 17:12 da sanyin Safiya bayan su Rilwan sunyi sallar asuba suka fara hira alokacin su sagir suka cire wayoyinsu suma suka hau facebook shikuma Rilwan yabude computer dinsa yayinda yake kwance akan gado yana gudanar da wani aiki. Wai nikam jiya kai da waye kuka zo kuka dameni da surutu tsakar dare? Rilwan yadan taso daga kishingidewar dayayi tareda ajiyar zuci, nahadu da wani gaye ne , wanda sana'armu tazo daya dashi. Atakaice dai munsaba dashi ajiyan nan shiyasa ma nazo dashi nan. Aikin banza shine zakuzo kuna tashinmu da hayaniya? Rilwan yace ah toh menene dan antasheku, hmmmm bakomai Allah yasa yau kusake yimana haka kugani wallahi daga kai har shi dakuwa zakuyi sagir yafada ransa a6ace, Rilwan ya tuntsire da dariya ni natuna ma yacemin zamu tattare kayakinmu daga hotel dinnan mukoma gidansa da zama. Gidansa kuma wane dan yaron?? Uhm nidai haka yafadamin sannan kuma yau zaizo muje nakalli gidan. Dakyau kace yaron manci ne mana? Yace kutt lalle kuwa ai sai kaga motarsa ma wallahi 307 sabuwa yake hawa. awwal yace wanne irin sana'a yakeyi? Hmmm sana'ar dana keyi . Anjima kadan zaizo yasameni muje, sagir yace toh ya batun Hajiya Fadila kuma? Yawwa inaga Hajiya fadila dinnan gara mushirya muje mata yanzu kawai tun kafin gari yawaye takarya kumallon safe da mu, alokacin tafito daga wanka tashigo cikin dakinta kai tsaye sai takallesa yana kwance asaman gado yadaura kafarsa daya akan daya, yana rikeda waya, idan kagansa zaka ce cikin dakinsa yake kwance. Takura masa ido sai kuma taga bata ganesa ba Hajiya fadila cike da mamaki tace yadai bawan Allah lafiya kuwa kashigomin har cikin daki batareda nasani ba? Ahankali yatashi yakalleta yawwa Hajiya sannunki da dawowa. Waye kai tajefamasa tambaya. Hajiya kenan kiyi hakuri kisami waje kizauna sai muyi magana dake? Idanunta duka akansa tazauna agefen gado bisa dukkan alamu hankalinta yadan tashi amma dayake tana da juriya hakan yasa bai baiyana afili ta tsorata dashi ba. Nasan kina mamakin ganina kai tsaye cikin dakin ki ko? Ta gyada kai alamar eh, toh kiyi hakuri da shigomiki daki danayi, sannan yacigaba dacewa akwai wasu yara Sagir da Awwal wadanda wani abu yafaru tsakaninki dasu wanda har sukayi miki sata suka gudu ko? Tace eh, yace ehen toh ni dan uwansu ne ina zaton sunta6a baki labari na sunana Rllwan . Tace toh sannu Rilwan yace yawwa Hajiya, wato sun fadamin abinda yafaru tsakaninku sannan kuma suka nunamin satar da sukayimiki, sai naji gabadaya abinda sukayi miki baidace ba sam sam amatsayinki ta wacce ta taimaka musu lokacinda basu dashi ba matsala bace idan sun biya miki bukatarki, tadan saki murmushi bisa dukkan alamu yanzu nitsuwa yafara shigarta, sannan kuma duk abinda suka dauka miki nakar6a kuma na dawar miki yanzu haka zalika ina mai baki Hakuri bisa wannan abinda suka aikata miki. Tace karka damu naso ace yadda kake da fahimta haka suke da ace haka suke da ba'a sha wahala ba. Sun wahalar dani kuma nasani suma sun wahala nasani kafisu wayo da sanin abinda yadace sabida haka babu abinda zanyi maka sai godiya, yace bakomai Hajiya yazaro ATM dinta dakuma wayarta yamika mata. Cike da mamamaki tadubesa dama harda ATM suka dauka ne? Kwarai kuwa sannan kuma zan baki hakuri sabida sun debi kudi acikin account dinki dan inaga kinta6a aikensu banki kuma da ATM dinki yanzu kudinda suka diba kadan ne wanda bai taka kar a yakarya ba. tayi ajiyar zuci sannan tace ni ai har nasayi wata wayarma layinma daman yanzu nake shirin zuwa yin welcome back yace toh yanzu kam dai gashi nan na hutar dake tayi murmushi sannan tayi godiya yayinda takuma hayewa kan gado tamatso kusa da Rilwan takunna wayarta din sannan tace Rilwan nagode sosai. Yace toh hajiya ni zan tafi tace no bazaka tafi ba sai ka tsaya kaci abinci yace ok badamuwa tashiga ciki tahada masa tea da indomie cikin sauri sannan takawo masa yakar6a yazauna yaci sannan yatashi zai tafi tace bazaka tayani zama ba ? Haba Rilwan wallahi hankalina yakama lamarinka nida tun farko dakai nahadu ma. Yadanyi murmushi Hajiya kenan toh nidai ina sauri yaza'ayi kenan. Bisa dukkan alamu wannan saurayin dan harka ne ba irin wadancan garorin ba dubi fa yanda yaketa kallona azuciyarta take sakar zance sannan Takatse zance da cewa bamatsala yakamata yau kawuni agidana yau ka shakatako? Ya danyi murmushi hajiya kenan wane irin shakatawa kinga nifa bana son 6oye 6oye kawai ki fito fili kafada min bukatarki? Tace dakyau tunda kafahimceni balalle bane nayi maka karin bayani, yace ok tashin farko ya cire rigarsa yaje yamike akan gado Hajiya tagama kintsawa tanufoshi sai taji anbude kofar dakin dasauri ta waiga dan takalli wanda yabude kofar , Sagir kuma meyakawoka gidana kafin tarufe baki Awwal ya biyosho abaya da sauri ta waiga takalli Rilwan ya tuntsire da dariya , Hajiya kenan kizo muyi mana yanaga kintsaya kina kallonsu inace wadannan gabadaya kinsansu Awwal ne da Sagir waye baisan Halinki acikinsu ba mekuma zaki 6oye musu? Tajuya takallesu babu alamar sakin fuska ataredasu. Hmmm mekuka shiryamin ne? Tajuya takalli Rilwan da kyau daukan fansa mukazo. Haba me kuma nayi muku wanda har zaku zo kuyimin wani abu? Dan Allah kuyi hakuri karkuyinmin komai dan Allah karku Kasheni tazo tadurkusa agaban Rilwan dan Allah kuyi hakuri. ha'a Hajiya munce zamu kasheki ne? Ni ai bakiyimin komai ba sai girkin dakikayi naci mekyau. awwal kikayiwa laifi kuma shi yakamata kije kidurkusawa kibashi hakuri bani ba. Tajuya wajen Awwal dan Allah kayi Hakuri Awwal Rilwan yace kije mana kusa dashi kamar yadda kikayimin inace kinfison zama kusa da jikin mutum cikin fargaba takarasa wajensa dan Allah kayi hakuri Awwal nayi kuskure, jitayi kawai ya dauketa da mari saida takallli taurari nayawo a sama kamar walkiya, sai da ta fadi har kasa. ta tashi yayinda taride kumatunta inda yamara din, Awwal nice yau nazama abin duka awajenka? Abinda yafi duka kikamin yabata amsa, ni da duka na din kikayi ai da zaifiyemin akan abinda kikamin, yakara daga Hannu zai kuma marinta Sai Sagir ya rike Hannunsa, kai bakasan cewa babu kyau dukan mace afuska ba? Ko ka manta ne ? Kaga Sagir kasakeni kawai ita abinda tayimin ya dace ne? sagir yace bazan sake ka ba. Nace bazan sake ba din kaga wannan matar fa zata Haifeka kuma kake mata irin wannan abin, and so what dan zata Haifeni saime Awwal yafada yayinda yafincike Hannunsa daga wajen Sagir, taresa yakuma yi Rilwan yace Awwal dakata ina tunanin akwai hukuncin da musulunci yatanadarwa duk wanda ya aikata zina, Sagir yace kwarai kuwa akwai. Rilwan yace yawwa bulala nawa ne ma akewa wanda yakeda Aure yayi zina? Ai ba bulala bane ma kisa ne fa? awwal yafada. Rilwan yace eh hakane fa Hajiya kinada Aure ko? Tace wallahi banda Aure narantse muku da Allah banida Aure, jikinta na 6ari na tabashi amsa, toh idan bakida Aurema ai akwai hukuncin wanda yayi kuma bashi da Auren ma. Bulala Nawa ne ma? awwal yace bulala dari ne, sagir yace a'a casa'in da biyar ne, suka kama musu awajen Rilwan yace toh tunda babu malami acikinmu kawai dari din zamuyi mata inma 95 din ne biyar sunzama gyara kenan.? hajiya tana kwance tana ji sunata lissafi dan Allah 'ya'yan nan kuyi hakuri natuba bazan sakeba. Rilwan yasaki dariya Hajiya kenan bakece nakalla A whatsAp naki sugar mummy ba? Tace wallahi ada ne amma yanzu daga yau na dena, Rilwan yace toh mudai zamuyi hukunci Sabida a yanzu haka yarataya awuyanmu mu hukunta ki. Akwai bulala ne? Yatambaya kai babu toh cire belt dinka kayi mata dashi, yace kai belt din nan bazai yi zafi ba, toh yaza'ayi nima nawa bamai zafi bane Sagir yace nima nawa hakane kawai kayi mata dashi din, tace dan Allah dan annabi kuyi hakuri Rilwan yace Hajiya mufa mun hakura amma hukuncin ubangiji ne sai mun zantar akanki, alokacin wayar Rilwan yafara Ringing yaduba yakalli Uziboy hello yafara magana eh yah ne mugu nazo site dinka bakowa kana ina ne? sai Rilwan yace ina wani waje ne nida 'yan uwana muna AKE novels / HAKAN TAKE part 22 HAKAN TAKE part 22 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 17:14 muna wani aiki ne anan amma please jirani 10 minutes kawai muna zuwa. Ok dan Allah kuyi sauri banason zama anan because area dinka akwai rescue gareni, ok karkadamu gani nan zuwa. Rilwan yakashe wayar Sannan yadubesu yace Uziboy yakirani yana jirana a site dinmu. Toh muyi mata hukunci da gaggawa kawai mutafi, Rilwan yace No mukyaleta kawai ko yanzu ma ai ka doketa, Awwal yace sam bazaiyiwu ba wallahi bazamu kyaleta ba ai saita sake nan gaba idan muka kyaleta yanzu, uhmm karka damu Awwal kazamo mai mancewa da duk sharrin da akayi maka wani lokacin kuskurene kuma kowa baifi karfin hakan ba,kadauka cewa sharrin shaidan ne yasa Hajiya ta aikata maka wannan abin, kasan dai kaima bakafi karfin sharrin shaidan ba ko? Sagir yayimasa bayani cikin nitsuwa , Awwal yadanyi ajiyar zuci sannan yace Sagir ko da kaine akayimaka wannan abin nasani ba kyalewa zakayi ba toh kuma meyasa kake ta nacemin akan na hakura, Sagir yadubesa tareda cewa ai da ni tayiwa wannan abin da kuwa tuni na kyaleta, ita da ubangiji, shin kai ko kamanta abinda mukayi wa Khairat ne? Shin Khairat bata yafe mana bane? Dubi mahaifinta yanda yadaukemu kamar 'yan uwanta, rike mana kanwa fa sukayi kuma kasani abinda yahadamu dasu kowa yaji yasani muba mutanenda zasu kar6i uzurinmu bane, jikinsa gabadaya yayi sanyi Awwal yasauke bulalar sannan yadubeta cikin kawaici Hajiya kitashi kawai nayafe miki kiyi hakuri, tadanyi shiru alokacin Hawaye suka kwaranya daga idanunta nagode Awwal ni ce yakamata na nemi gafara awajenka, nasani yanzu haka nabude maka kofa bansan wane irin bala'i zaka shiga nan gaba ba dan Allah kayi hakuri nayi muku alkawarin daga yau nadena, Rilwan ya dan saki murmushi toh Allah yashiryemu gabadaya, suka ce ameeen, Awwal yazo yadurkusa yace Hajiya kirama marin danayi miki, tace bazan rama ba duk abinda kayimin yanzu kamata yayi ma ace nabiyaka kudi sabida ayanzu nafahimta cewa haduwa ta daku alheri ne, nagode Allah yasaka muku da alheri wayata ma dakuka dauka na baku ita kyauta kudina ma dakuka dauka shima nabaku kyauta, sannan kuma akwai kamfanin da zan gina nayi muku alkawarin zan damka muku komai na wannan kamfanin ku kulamin dashi, Rilwan yace Mungode karki damu Hajiya zamu rika kawo miki ziyara muna gaisawa, yanzu muna sauri sabida haka zamu tafi, tace nagode Allah yakiyaye hanya, suka fita daga gidanta suka tare mai adaidaita yakaisu kofar hotel din, yana zaune acikin motarsa yana chattin suka sameshi ganin sun iso ya ajiye wayar sannan yabude motar yafito ya akayi ne legend yafada ma Rilwan Uziboy suka tafa sannan yamika ma su Awwal Hannu suka gaisa daga bisani yace almost 30 minutes fa ina jiranka anan, Rilwan yace sorry bross aikin ne yayi yawa shiyasa, Uzairu yace toh yanzu sai muje gidan kagani ko? Rilwan yace ba matsala ko zamutafi tare daku ne? Awwal yace no nikam zan shiga nahuta sai kundawo Sagir ma yace yagaji zai huta, suka kama hanya su biyu kai tsaye suka tafi can gidan a Unguwar GRA babban gida ne yasha gini irin na zamani Rilwan yazura idanu tako ina a sassan gidan Uziboy na your house be this? Yes yafada make you enter naw yafada masa zance cikin turancin inyamurai, suka wuce Rilwan yakalli nan yakalli can suka shiga cikin falo kai tsaye, uzairu yafara kira NetMaye kana ina ne? Yazauna eh uziboy gani nan anan ya amsa daga cikin dakin, yabude kofa yafito sanye yake da singileti da gajeren wando yakaraso inda suke yamika ma Rilwan Hannu Rilwan ya kura masa idanu idan ban mantaba nata6a ganin gayen nan awani waje yatambayi zuciyarsa? Abokina kamar nata6a saninka awani waje fa? Yajefawa Rilwan tambaya, eh kwarai kuwa nima tunanin danakeyi kenan amma namanta da ko a ina ne? Inaga kamar tafiya mukayi muka shiga mota daya ko? Rilwan yace haka kwarai kuwa haka akayi daga adamawa zuwa jalingo ko? Yace eh kwarai kuwa ni namanta kafadamin sunanka ko? Yace eh sunana Rilwan kaikuma Abdul ko? Yace eh kwarai kuwa amma zaka iya cemin Netmaye, dakyau net maye yamika masa Hannu suka tafa, uzairu yace oh guys ashe kunsan juna ma, eh kwarai kuwa suna zaune saiga wasu 'yan mata sun fito daga dakin da Netmaye yafito, Rilwan yabisu da kallo, uziboy yace yadai bross ko wata ta cijeka acikinsu ne? Rilwan yace No me sukeyi anan ? Yatambaya, Uziboy yadan saki murmushi sannan yace tambayi Netmaye wadannan chiks dinsa ne Rilwan yasaki murmushi gaskiya ne Netmaye kana shagalinka, yace bakomai kaima zaka iya ai. Rilwan yace no ni bana saka mata a harkana , netmaye yayi dariya yace hmmm baka zauna dasu na wani lokaci bane idan kazauna dasu zaka fara kaima, yace toh ni idan zanyi ma bazan wuce soyayya ba kuma daya kawai zanyi soyayya da ita infact bazan fara ba ma sai natashi Aure, hmmm bari nashiga ciki nafuto Uzairu yatashi yabarsu awajen suna tadi sannan yafito yace yawwa bross yakaga gidan? Rilwan yace gida yayi kyau sosai wallahi, kaga dakuna harda na banza kawai kai da 'yan uwanka kudawo nan yafada, Netmaye yace eh namanta fa bantambayeka 'yan uwanka ba? Yace suna nan zamu zo dasu nan zamu dawo, yace goood daman ina fama da kadaici Uziboy sai yawo kamar shansani , badan 'yan matan nan bama da kadaici yamin over, yace karka damu idan suka dawo shin zaka dena harka da 'yan mata? Yace No ai mata sune abokan rayuwa idan babu su babu morewa, uhmmm nidai duk wannan abin bansan dashi ba Rilwan yafada yayinda yatashi yace nizantafi zamu dawo da kayakinmu anjima, Uziboy yace toh bamatsala zanzo nadaukeku damota sabida akwai nisa, Rilwan yace No problem yatashi zai tafi Netmaye yace bari muje mana bross suka kama hanya, Netmaye shima da motarsa sukaje suka shiga Rilwan yace nifa abinnan yana bani mamaki wai acikin wannan harkar ta YY kuka sami wadannan kudade? Netmaye; kwarai kuwa shin kai kana nufin baka da ko mota taka takanka? Rilwan yace ina naga mota ko mashin banida , netmaye: karka damu baka gane taku bane akwai salo da muke da ita nadaban, sannan kuma yana dakyau idan zakayi harka irin wannan kake hadawa da Malamai sannan ko matsafa haka. Rilwan sai daya firgita tsafi fa kace, yace yes idan ba tsafi ko kuma rokon Allah ya zamuyi musami wadannan kudaden? Idan bazaka iya zuwa wajen boka ba akwai malamai kaje kasamesu kabasu abin sadaka suyi maka addu'a zaka ga canji acikin harkarka, da kyau gara hakan amma kacemin boka ai abu baiyiba kasan hukuncin wanda yaje wajen boka a addinin musulunci kuwa? Menene basai kamutu za'ayi maka hukunci ba? Netmaye yafada. Rilwan yace Eh, sai yace ai zakazo katuba idan katara sabida haka kawai kamanta da komai kanemi kudi awannan zamanin idan baka da kudi wallahi zaka sha wahala fiyeda yadda kake tunani? Har suka iso suna ta hirar. Bayan sunje Su sagir suka gaisa da Netmaye sannan suka kwashe kayakinsu daga Hotel din suka koma gidansu Uziboy. Gidane babba kuma akodayaushe bazaka rasa mace agidan ba kasancewa gidan samari ne kadai shiyasa matar banza keta kaiwa da kawowa agidan. A6angare guda kuma Aisha tana zaune acikin daki yayinda khairat ke rike da wayarta ahannu tareda wani takarda bisa dukkan alamu tana wani rubutu ne wanda yakan iya kasancewa assignment ne da aka basu amakaranta. alokacin saiga Sani yashigo cikin dakinsu yace Khairat ke ce kika dauka min waya ko? Yace a'a bani bane, toh waye zai dauka tace nima bansani ba. Yace bani wayarki nagwada tace wayana baya nan. Nabarshi adakin Umma. Ok ka kar6i wayar Aisha kagwada yace ok ina wayar tadin yake, Aisha tayi Nuni da kusa da tv gashi can akusa da tv yana chaji, yace ok bari nadauka nakira layin, yaje yacire dubawar dazaiyi sai yakalli hotonsa afuskar wayar ha'a yadai Aisha kuma Aina tasami wannan hoton yatambayi kansa baisan amsarba yadaga kai yakalleta ita batasan ma yana kallonta ba, ita ko Khairat ta zuro masa idanu yadai Hamma? Yadanyi murmushi babu komai. Sannnan yasaka lambarsa abinda yabashi mamaki sunan da yaga anyi saving din lambarsa dashi, My hope yaga anrubuta akan lambarsa baisan lokacin da yafitar da zancen ba My hope kuma? hamma Sani yadai kagwada wayar baishiga bane? khairat takatseshi da tambaya.dasauri yadawo daga nazarcen dayakeyi. Ya danna calling wayarsa sai yashiga abin mamaki sai yaji wayar tana Ringing akusa da inda Aisha take, Sani yajuya yakalli khairat wato ke kika daukomin waya kuma kikacemin bakeba ? Tadan saki murmushi Hamma kayi hakuri namanta ne Aisha mika masa wayar, Aisha ta tashi tareda rufe littafin datake karantawar sannan tasaka hannunta tadauka batareda tace wani abu ba, sunan data gani anyi saving na lambarta yahaddasa mata mamaki acikin zuciyarta, My dream taga an rubuta akan lambarta awayar Sani tayi ajiyar zuci sannan takatse kiran tamika masa wayar zuciyarta cike yake da mamaki me yake nufi da My dream, Har yakarbi wayar kallonsa takeyi har cikin idanunsa yayinda shima yakura mata idanu, sun dauki 'yan dakikai kafin nan Khairat tayi Gyaran murya sannan Sani yasaka Hannu yakarbi wayar yana faman mika mata nata, Khairat tace Hamma kamanta ne a caji fa kacire wayar kuma nasan bai cika ba. Yace oh sorry yakoma yasaka mata acajin kafin nan yafita zuciyarsa cike da tunani bai tsaya yatambayeta abinda take Nufi da sunan ba, haka itama tunani yamamayeta tabisa da kallo har yafita daga dakin. khairat tace yadai nakalli gabadayanku jikinku yasauya ne wai me yafaru ne? Aisha tayi ajiyar zuci sannan tace hmmm babu komai , khairat tace toh nidai gaskiya keda hamma kuna 6oyemin wannan abin kuma alhalin nasani.. ni nayi miki alkawarin saina hadaku soyayya atsakaninku tunda dukanku 6oyewa junanku kuke gashi kuma naga alamar tun kafin nafara koyama jariri tafiya har yana koyan gudu. Uhm me kike Nufi da wannan zancen Khairat? Hmmmm akwai mana Khairat tafada sannan tace nangaba Hamma shida kanshi zaizo yanemi soyayyarki kuma ina kaiki wajen, Aisha batace komaiba sabida azuciyarta taga alama, shima Sani cike damamaki yakoma dakinsa wai yarinyar nan haka tayi Saving din sunana my dream? Hmmm toh ko me take nufi da wannan kalmar oho, uhmm gaskiya yakamata inji dalilin fadar wannan kalmar, amma 'yar sa'idon nan bazata kyaleni natambaya ba, hmmmm kodayake wata kila ma tasan komai kawai shiru tayimin kai amma khairat zaiyi wuya tasan da wannan bata sanar dani ba. Kai duk yadda za'ayi sai na tambayi Aisha wannan dalilin, yakwanta akan gadonsa hmm wannan yarinyar da kwarjini take? Ko me yasa ban tsaya natambayi dalilin sunan nan bane? Aisha aranar kusan kwana tayi tana tunanin wannan sunan, washe gari dasafe bayan sunyi karin kumallo, Khairat tashiga wanka Sani ya lura da hakan alokacin sai yadauki wayarsa yakira lambar Aisha tadauka yace kina inane? Tace ina daki sai yace toh kifito inason magana dake awajen da muke parking na motoci, tace ok gani nan zuwa, ta dauki hijabinta tasaka sannan tanufi wajen daya sanar mata yana wajen, tasamesa yana zaune agaban mota takarasa inda yake tareda sallama ya amsa . Sannan yace mata sami waje kizauna so nake intambayeki dama, tadanyi ajiyar zuci toh ina sauraronka? Yace jiya nakar6i wayarki nakira lambana sai kuma nakalli abinda yabani mamaki, tadafekirjinta mekagani Hamma? Yace naga sunan da kikayi saving din lambar dashi ne ? Ta danyi murmushi ai sunanka ne dama uhmm hamma sani kenan wannan shine kadai dalilin dayasa kakirani nan wajen, yace kwarai kuwa me kike Nufi da kalmar my hope? Cikeda mamaki tace my Hope kuma? A ina kuma kaga my hope ? Yadanyi murmushi hmmm kina nufin kicemin kinmanta sunan dakikayi saving na lambana dashi? Tace Ni dai Hamma Sani nasaka akan lambarka. Yace hmm Aisha zakiyimin Musu bari nagwada miki lambar mana kigani, yaduba zai dauki lambarta sai kuma baiga sunan dayayi saving din lambarta dashi ba. Aisha yayi searching amma babu sunan, sai yace inaga nayi missing lambarki ki kira min lambar muji, tace kaduba call entries mana ba jiya kakira lambarka da da wayana ba. Yaduba call entries baiga sunan Alsha ba sai kawai yakalli my dream acikin call entries din toh nidai bansan lokacin da wannan lambar yashigo ba.sabida haka bai gaskata abinda idanunsa suka nuna masa ba, sai kawai yace mata babu kawai ki kiramin lambar, sai tafara kira masa yana sakawa yana ganin lambarta yana matching da lambar da aka rubuta my dream akai, har yagama yakalli lambarta ne aka sanja sunan shidai yasani bashi yarubuta wannan sunan ba duk da haka sai yaki yanuna alamar wani abu sai ya danna kira alokacin yashiga wayar Aisha sai yace duba kigani tana duba sai taga incoming call from My Hope, my Hope kuma? tafada azuciyarta, yace mekike sakawa acikin ranki mikomin wayarka nagani nima tabashi amsa ba musu yamika mata itama tamikamasa nata saitaga lambarta yana nan a my dream. Shima yaga my Hope. Alokacin saiga Khairata tafito tana murmushi tana tafa hannu yawwa yaukam idanuna sun ganemin ashe dama atsakaninku akwai ,N TAKE novels / HAKAN TAKE part 23 HAKAN TAKE part 23 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 17:16 Aisha tawaiga takalli Khairat tana dariya murmushi tadan saka Sani kuma yace toh fadi abinda kikeson fadi tsakaninmu akwai me? Khairat tace uhm kunfini sani ai gaskiya Hamma nayi maka murna da kasamu mace kamar Aisha, yace ke Khairat wai ke wace irin mara kunya ce? Na fahimci abinda kika shirya ayanzu wato kece kika dauki wayana kika canza sunan da nayi saving din lambarta dashi sannan kuma kika dauki wayarta kika sauya sunan datayi saving na lambana dashi, hmmm wayagayamiki ana nuna wa ido bacci? Kyalkyalewa Khairat tayi da dariya sannan tace ashe kagane abinda na shirya kuma tarkona yakama, uhmm lalle kuwa tarkonki yakama Aisha kunya yakamata tajuya zata gudu awajen Khairat tarike hannunta sannan tace ai baki isa ba wallahi, dan bangama ba, Aisha tajuya kisakemin hanuna nikam, Khairat tace anki asakeki din. sani yace saketa mana Khairat tace zan saketa amma sai kabani amsa tambayar dazanyi maka yanzu. Yace kinga nifa ba abokin wasan ki bane, tace Hamma wallahi ko kasheni zakayi sai dai ka kashe, amma sai ka amsa min tambayar dazanyi maka, yace toh fadamin tambayar? hamma inaso kafadi tsakaninka da Allah baka son Aisha acikin zuciyarka ? Yaji zuciyarshi tayi wani irin sarawa ke bazan amsa miki tambayar ba saketa ta tafi. Alokacin Aisha taja hijabinta tareda rufe fuskanta . Ai bazan saketa ba sai ka bani amsa, jitayi kawai Aisha tafincike Hannunta ta ruga da gudu zuwa ciki, ji sukayi dariyan Hajiya yafito fili basu ankara da cewa ta 6uya tana jinsu ba. khairat tace Umma kinga abinda nake fadamiki dinko? hajiya tace kwarai kuwa nagani, Sani yace umma wallahi wannan fa duk shirin Khairat ce, zakacemin shirin Khairat tun kafin Khairat tafito nake 6oye anan wajen ai naji zantukan ku, Toh shikenan umma ni ban isa nazauna muyi tadi da ita ba sai ace soyayya muke? Tace toh me aciki? Kai kam ba namiji bane sai kace bazakayi aure ba? Yace zanyi mana Umma kinsan ai komai nada lokacinsa. Toh ai yanzu ne lokacinka din idan kace bazakayi ba kuma nangaba zakazo ka wahala sabida ba lokacin ka bane. Yace toh Umma ni ai bazan 6oye miki komai ba idan natashi aure kizaki za6amin matar da zan aura, ni ai Aisha naza6a maka kuma zan kira ta insanar da ita , sannan kuma idan Alhaji yazo shima zan sanar dashi sai atara jama'a kawai a shafa fatiha. Sani ya kyalkale da dariya sannan yace toh Allah yakyauta . Hajiya tace ameeen. A6angarensu Rilwan kuma bayan sun dawo da kayakinsu gabadaya gidan Uziboy, nan suka fara aiki ba tsayawa, uzairu yace ma Rilwan bross yakamata ka hadar da kanka? Rilwan yace bangane in hadar da kaina ba? uzairu yace idan kanaso akwai wata mata mai bada magani sannan kuma tana bada taimako sosai musamman irin wannan harkar tamu, na tabbata idan kaje wajenta kaima zaka samu harka sosai kamar namu din nan. Rilwan yace banfahimci bayaninka ba kana nufin idan naje wajenta akwai maganin da zata bani naje nayi ne? Yace kwarai kuwa wasu sharuda zata baka sannan kuma tahada maka da wani magani Rilwan yace muje wajenta anjima idan naga zan iya toh idan kuma naga bazan iyaba sai in hakura. Jim kadan suka shirya suka tafi da Uzairu sukaje wajen matar bayan sun gaisa take tambayarsa wannan abokin kane? uzairu yace Eh yanaso abashi taimako ne gameda sana'arsa tace toh ya sunanka ta tambayi Rilwan yafada mata sunansa tace toh malam Rilwan abubuwan danakeso kayi sunada yawa kuma sunada wahala. Dafarko zaka zauna na sati 2 batareda kaje ko ina ba kana cikin daki kana karance karance. Sannan kuma zakayi azumi na sati 2. Bayan ka gama sai ka kawo abin yanka azubarda jini shikenan idan akayi haka zakaga canji a sana'arka. Rilwan yayi ajiyar zuci gaskiya matarnan ta debo abin da wahala yafada azuciyarsa sannan yace toh in Allah ya yadda zanyi komai amma yanzu zan koma sai na shirya sai nadawo afara aikin tace toh shikenan suka tashi Rilwan yadauki Naira dubu daya yabata tace yabar kudinsa kawai sai angama yimasa aiki. Sukayi godiya sannan suka tafi ahanyar dawowa Rilwan yace ma Uzairu gaskiya ni bazan iya azumin sati 2 haka kawai ba. Uzairu yace sabida me shin bakaso kasamu biyan bukatarka ne? Yace inaso amma bazan iya ba kai nifa ko a ramadan dinma dakyar nakeyi sabida bana iya juriyar yunwa gashi kuma ina da ulcer amma wannan haka kawai inyi ta azumi ba lada sam bazaiyiwu ba. Uzairu yace toh shikenan tunda bazaka iya ba sai ka hakura. Rilwan yace gaskiya hakuran zanyi idan inada rabo zan ha6aka sosai kobanyi wannan tsubbe tsubben ba. Suka iso gida alokacin suka sami su Awwal suna kallo afalo uzairu kai tsaye ya wuce daki, Netmaye yace kunsami matar Rilwan yace eh munsameta amma ni bazan iya yin abinda tace ba. Netmaye yace me tace maka? wai zanyi azumin sati 2 nikuma bazan iya ba. Netmaye yace karka damu akwai wani malamin da zamuje wajensa yana istihara kuma yana bada rubutu sannan kuma yana yin addu'o'i shi kam babu wani abinda zaice maka kayi. Rilwan yace toh sai muje anjima ko? Netmaye yace toh bamatsala jim kadan suka kama hanya sune basu Tsayaba sai gidan wannan malamin suka shiga sukayi sallama alokacin yana ciki sabida haka yasa yaturo yaro yace yana zuwa , suka zauna acikin zaure suka jirashi jim kadan saigashi yazo suka gaisa sannan Rilwan yayi masa bayanin abinda yakawo su. Sai malam yace toh ba damuwa yanzu abinda nakeso dakai kaje ka kawomin abin sana'arka din tunda kace da computer kake sana'ar kaje kakawomin computer dinka tayi kwana 1 anan idan takwana washe gari sai kazo kadauka sannan kuma kasayi wani abu sai ka rabawa yara amatsayin sadaka. Rilwan yaji dadi sosai kasancewar baiji wani abin wahala da malam yafada masa ba sabida haka yasa yadawo gida yadauki computer din da sadauki yabashi sannan yatafi da computer din yakaiwa malam. Malam yace gobe kadawo ka karbi abinka Rilwan yayi godiya sannan yafita. Washe gari da safe Rilwan yayi sammako zuwa gidan malam yatura yaro malam yafito sannan malam yace yawwa kadawo ba Rilwan yace eh malam yakoma ciki yadauko computer din yakawo masa sannan yace Rilwan akwai abinda namanta ban fada maka ba sabida haka saika kula da wannan computer din sosai kaga abinda nayi maka din nan sau daya kawai akeyiwa mutum arayuwarsa. Idan kayi wasa da wannan damar babu halin sake dawowa sabida haka sai ka kula da wannan computer din taka. Yace toh malam nagode sosai insha Allahu zan kula dashi sosai yadauki naira dubu hudu yabawa malam sannan yayi godiya Rilwan yatashi yatafi. Alokacin lissafi suka fara kwancewa Rilwan ko ta ina yabi a net sai ya samu kafin wasu 'yan lokuta Rilwan yasamu kudi fiyeda kima wanda hakan yasa shima yasayi mota sannan kuma yajawo 'yan uwansa dukansu zuwa cikin harkarsa din. Wata rana suna zaune acikin falo wasu 'yan mata suka shigo Rilwan kafin ya ankara daya tayi awongaba da hankalinsa kallonta kawai yakeyi, netmaye daga nesa yace haba bross irin wannan kallon haka? Rilwan yasaukar da kansa tareda murmushi Netmaye yabudema 'yan matan kofa suka shiga dakin sannan yarufe yadawo wajen Rilwan yace acikinsu wacece tayi maka. Rilwan yace wannan 'yar daidai dinnan wacce tasaka jan riga, Netmaye yayi dariya sannan yace zulibaby kenan? Rilwan yace sunanta kenan? Netmaye yace kwarai kuwa karka damu zan hadaku da ita kawai Rilwan yace da kyau da ka kyauta bross. Suka tafa sannan Netmaye yawuce cikin daki Rilwan yacigaba da aikin dayakeyi a computer. Jim kadan saiga wannan budurwar tafito tazauna akusa da Rilwan tace sannunka da aiki ya amsa mata yawwa taciga da cewa Netmaye yayimin bayanin komai kuma nayi farin cikin hakan Rilwan yadanyi murmushi sannan yace toh nikuma ina godiya sosai. Tace yawwa suka zauna awajen suka kama hira Awwal yafito yasamesu yacema Rilwan wannan fa? Kai tsaye Rilwan yabashi amsa yarinyana ce ita, awwal cike da mamaki kafara neman mata ne kaima ? Yace eh wallahi amma kuma nakusan Aure, zulibaby tace waye zaka aura Rilwan yace ke mana. Tadanyi dariya sannan Awwal ma abin yabashi dariya yazauna suka cigaba da hira, da dare misalin karfe 11 Rilwan yadawo daga club yashigo dakinsa sai yakalli zuli tana kwance akan gadonsa sai shekar bacci takeyi. Baice mata uffan ba yakoma gefe 1 na gadon shima yakwanta cikin kankanin lokaci bacci yayi awon gaba dashi wayar Rilwan tafara Ringing hakan yasashi farkawa daga bacci dubawan dazaiyi yakalli lambar Sadauki dayake amfani da ita na nigeria hakan yatabbatar masa dacewa Sadauki yadawo najeriya ,take yaji gabarsa yafadi yadauka tareda sallama oga barka da warhaka. Yace haba Rilwan tun jiya naketa gwada lambarka bana dacewa wai meyasa kake kashe wayarka ne? Rilwan yace wallahi oga akwai rikicin dana 6aro ne shiyasa bako da yaushe nake barin wayana akunne ba. Sadauki yace da kyau dama nadawo ne shiyasa nakira insanar maka bansami wayarkaba naje camp loveth hotel ma naga alamun ka kaura awajen. Rilwan yace eh wallahi yanzu haka ina unguwar GRA sadauki yace toh turomin Address dinka zanzo gobe domin inada bukatar computer dina ina fatan kaima yanzu yaci ace kasayi naka, Rilwan yadanyi shiru yana tunani idan sadauki yakar6i computer dinnan yatalautar dashi kenan domin duk cigaban dayasamu da wannan computer din ne da hanzari yakatse tunaninsa sannan yace oga ansami akasi computer dinka nasayar da ita. Sadauki yace mekace yazaka sayar da computer dina batareda iznina ba? Yace oga wallahi matsala ne tafaru computer din ya6aci naje wajen gyara akace bazai gyaru ba sabida haka sai muka shirya nasayar musu ita sabida akwai abubuwa masu amfani ajikinta. Sannan nasayi sabuwar computer na ajiyeta musamman domin idan kazo inbaka ita amadadin wancan, sadauki yayi ajiyar zuci sannan yace toh naji shikenan kashirya gobe inazuwa karka kashe wayarka, Rilwan yace toh bamatsala sai kazo yakatse kiran sannan yazauna yana tunanin mafita take yayi ajiyar zuci sannan yace ai nagama dashi tunda ya yadda kuma ya hakura da sayarwan danayi din. Dasafe Rilwan yatashi misalin karfe bakwai yafita har wannan lokacin zulibaby tana sharar bacci ko uffan baice mata ba yadauki key din motarsa yafita kai tsaye yaje yasayo sabuwar computer sannan yadawo alokacin yasameta tafarka takunna tsohon computer dinsa tana kallon wani film yace mata sarkin bacci kin farka ne. Tace eh, yazo yazauna kusa da ita shima yafara kallon film din alokacin sai ta jingina da jikinsa batareda ya ankareba kawai yaji tana faman shafe jikinsa yadubeta zulibaby why? Tace i am fond of you dear cikin kashe muryam,, yadanyi murmushi baisan lokacinda shaidan yashiga zuciyarsa ba kawai yasake mata jiki tafara balle botin din rigarsa tacire ta ajiye agefe shiko kamar da asiri sai lumshe idanu yakeyi, alokacin wayarsa tafara ringing yace mata excuse me yaduba yakalli sadauki ne yadauki kiran Sadauki yace ganinan akofar gidan daka bani address dinta. Rilwan yace toh ka kariso ciki sadauki yashigo kaitsaye alokacin Rilwan ya dubi zuli baby i am sorry bari naje najida ogana tukunna tace toh sai kadawo. Yafito sanyeda gajeren wando da singilet yasami sadauki yana zaune afalon gidan yazo da gudu oga oga har ka isone , sadauki yace kwarai kuwa na iso Rilwan yace da kyau oga indiyan nan ya kar6e har ka karayin haske Sadauki yayi dariya sannan yace anan kakeda zama? Rilwan yace Eh wallahi sadauki yace gaskiya kayi kokari katara fa awannan harkar Rilwan yace Allah ne yake badawa ai, sadauki yace eh sannan kuma kaima dana ka dabarun ai. Rilwan yadanyi murmushi sannnan yatashi yadauko ma Sadauki drinks yazuba masa. Sadauki yafara sha alokacin yatambayesa ina sabuwar computer din dakace kasayamin din? Rilwan yace yana cikin daki bari naje nadauko maka, yatashi yashiga yasameta takuma kunna tsohon computer din tana kallo. Baiyi mata magana ba yadauki sabon computer din sannan yafito ma sadauki dashi Sadauki yakar6a yabude yace gaskiya Rilwan kasami kudi sosai wannan computer din kamar ba'a ta6a aiki da ita ba. Rilwan yace eh sabuwace Sadauki yace dakyau wato a indiya na hadu da programmers dayawa, wadanda suka karamin ilimi sosai afannin computer Sadauki yabude chapter din Hira Rilwan yakasa kunne sai kawai yaji sautin tafiya yana fitowa daga dakin daya fito dincan basai angaya masaba yasan zuli baby ce take fitowa, da tsohon computer din ahannunta tana cema Rilwan my love nagama kallon 1 din wannan film din saura 2 kuma nasara inda 2 din yake. Sadauki yadaga kai yakalleta sanye take da dan karamin riga sai kuma gajeren siket wanda har cinyarta awaje suke. Rilwan yadoka mata harara ta kura da kallon dayayi mata sabida haka tafahimci abinda yake nufi saita juya takoma dakin.. sadauki yadubi Rilwan wancan ba computer na din can ba? Rilwan yadan sosa kai yace eh shine wato bari in fada maka gaskiya oga wannan budurwata ce kuma nayi mata kyauta da computer din ne idan nace tabani kayana abinda kunya . sabida haka ne yasa nasayi maka sabo amma kayi hakuri oga, sadauki yatashi ransa a6ace haba yaro haba banta6a tunanin zaka rainamin hankali irin haka ba. Ni kuma zaka nunawa irin wannan cin amanar kayi kyauta da computer dina batareda izinina ba toh sam bazaiyiwuba ni bazan kar6i sabuwar daka saya dinba computer dina nakeso. Rilwan yadanyi kasa damurya dan Allah kayi hakuri oga karka sa naji kunya, sadauki yace what ai ni yanzu tsakanina dakai ba sassauci tunda ni zakayiwa irin wannan abin duk yanda za'ayi akwai abinda ka6oyemin. Rilwan yace babu komai oga kayi hakuri. Alokacin netmaye yafito daga dakinsa sai yaji su Rilwan suna hayaniya yafito yatambayi dalili Sadauki yasanar masa, netmaye yadanyi shiru yatuna cewa malam yafada musu wannan abin sau daya akeyiwa mutum arayuwa sannan kuma Rilwan da tsohon computer din akayi masa idan kuma sadauki yatafi dashi tofa takarema Rilwan cikin nitsuwa yake magana yace kayi hakuri maigida kakarbi sabon nan karkabashi kunya awajen masoyiyarsa. Sadauki yace sam bazaiyiwu ba yatada musu rikici zuli baby taji anata rikici ta nitsu taji abinda ake cewa saita fito da computer din takawo ranta a6ace my kabashi computer dinsa yatafi akan wannan tsohon na'urar nema zaizo yatayarwa mutane rigima agida Rilwan yajuya kamar zai wanketa da mari, mtsssw oh shitt women are the source any problem. Yace ki mayarmin da computer daki sadauki yace mata naji bani tsohon abina ai da tsohon yakoya har yakai matakin dayake yanzu, Rilwan yazo yashiga tsakani suna faman bada hakuri sadauki sai bude murya yakeyi. Hakan yasa Uziboy farkawa daga bacci sannan su Awwal da sagirma suka farka bayan sun fito sukaga netmaye da Rilwan suna ta bawa Sadauki hakuri yaki Hakura uzairu yazo yace kabashi computer dinsa yabar gidan nan Rilwan yace no gara yayi Hakuri kafin kace me Awwal yakar6e computer din ahannun zuli yamikawa Sadauki yace idan wannan ne computer dinka jeka kawai Rilwan yaje zai tare Sadauki Uzairu da sagir suka taresa haba me kabi kadamu akan computer tsohuwa mutum yazo yana ta cimaka mutunci har gida Netmaye yace bazaku gane bane wallahi akwai matsala . Sadauki yatafi da computer Rilwan yazauna yayi shiru sannan kawai yatashi yanufi daki yasami zuli tana kwance akan gadonsa, ke dan ubanki fitamin adaki, yafada tatashi lafiya kuwa my love kake korata? Yace bansani ba, yacire belt dinsa yatafka mata tayo waje tagudu yabiyota su uzairu suka rikesa yakake dukanta yace ba duka kadai bama zanyi mata idan nasake kallonta agidannan ma sai na karya mata kafa.E novels / HAKAN TAKE part 24 HAKAN TAKE part 24 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 18:26 kwanaki kalilan bayana sadauki ya kar6e computarsa, nan fa al'amura suka fara ta6ar6arewa ma Rilwan ya dauki computer dinsa sabuwar da ya saya din yafara aiki da ita amma sam ina abin baya tasiri. Komai dinsa ya fara komawa baya baya. Amma dukda hakan bai nuna damuwa afili ba saidai abin yana matukar damunsa acikin ransa domin kuwa kusan kullum idan ya kwanta bacci sai yayi mafarki sadauki yadawar masa da computer dincan. Damisalin karfe 3 na yamma yana kan computer yana faman bincike ashafin twitter sai yaji wayarsa tana ringing ahankali yamika hannunsa yadauka jikinsa amace. Wonderfull yafada yayinda yaga sunan khairat yabayyana a fuskar wayar. Hello .. Yafada cikin zumudi ta amsa suka fara magana, dafatan dai kuna lafiya khairat tajefa masa tambaya lafiya lau yasu ummanki da abba? Lafiyansu lau ya su awwal da Sagir ? Suma lafiyansu lau yabata amsa, da kyau ina Aisha take? Uhhmmm gatanan muna tare da ita. Yadanyi murmushi nasan za'a rina ai bata wayar muyi magana, toh tafada sannan tamikawa Aisha wayar ta karba tareda karawa akunnenta hello yaya Rilwan kwana biyu shiru kun dena kiranmu, kibari kawai Aisha ayyuka ne sukayi mana yawa. toh yaya Rillwan ai Haka akeso yaya ya aiki? Yace aiki alhamdulillahi yasu yaya Awwal da sagir? Yace lafiyansu lau, ina labarin lawwali maishago da su Bilal da fatima? Ya sake jefa mata wani tambayar, Lafiyansu lau jiya ma munje wajensu nida Khairat. Yace da kyau haka akeso kullum kirika zuwa kina dubasu kinlji? Tace toh yaya Rilwan yaushe zaku dawo? Ya dan saki dariya gaskiya zamu dade kafin mudawo saidai muzo mudubaku mu koma. Toh yaushe zakuzo kuduba mu din? Yace karki damu bazai dadeba zamuzo tace toh Allah yakawo ku lafiya. Yace ameeen. Sannan tamikawa Khairat wayar batareda ta katse kiran ba. khairat takarba tareda karawa akunnenta tasake cemai gaskiya yakamata kuzo kodan kukallemu, tun tafiyarku har wajen 1 year fa? Hakane kam wallahi aiki ne yarikemu, tace toh amma intambayeka mana wai wane irin aiki ne kukeyi haka? Rilwan yayi murmushi sannan yace kwantar da hankalinki ba kidnapping mukeyi ba. dariya yakufce mata sannan tace ai dama ni bance kidnapping kukeyi ba. Yace toh mudai yanzu aikin computer mukeyi. Wane irin aikin computer kuma? Yace oh khairat akwai ki da tambayoyi tamkar mai neman rahotanni, mun bude shago ne wanda muke buga littafi sannan muna photocopy da irinsu laminating da sauransu. Ayyo abin yayi kyau wallahi irin sana'ar yana birgeni. Uhm tukunna ma kudai cigaba da yimana addu'a kunga idan mundawo sai mu bude shagon agarinmu ko? Tace da kuwa kuntaimakawa mutane dayawa wallahi. Toh sai ku taimaka da yimana addu'a. Insha Allahu zamuyi muku addu'a, tamaida masa zance, sannan Rilwan yace namanta bantambayeki yayanki Sani ba ina fatan yana lafiya? Tace lafiyarsa kalau nima namanta banfada maka wata magana ba. Yace toh wace magana ce. Toh zan iya cewa alfarma zan nema awajenku gabadaya bansani ba ko zan samu. Rilwan yace haba Khairat har kina tunanin akwai wani alfarmar dazaki nema awajenmu bazaki samu ba? Tace eh toh bansan ya zaku dauki abin bane. Rilwan yace toh ina sauraronki. Sai tace ko kuma kaikam sai anjima zankiraka natambayeka. Sai ta katse kirar batareda tabashi daman yin magana ba. Hello hello khairat yafada yayinda yaji ta katse kirar, wannan kuma wane irin alfarma ne? Ya kira lambarta sai kuma yaji wayarta akashe. Hmmm lalle kuwa wannan yarinyar me take nema ne yau kuma? Hmmmm yana ta sakar zuci alokacin yaji anbude kofa Uziboy yashigo ya dai kaida waye kake waya haka? Rilwan Yace nida kanwata ce shine naji kanata zance kai kadai bayan ka gama? Hmmmmm bari kawai ai ni yanzu damuwa duk tabi ta isheni wallahi, uzairu yayi ajiyar zuci sannan yace shine matsalar neman taimako acikin harka. Yanzu haka da bakaje wajen malamin can kanemi taimako ba da yanzu babu ruwanka dashiga matsala uzairu yamaida masa zance Rilwan yace karka damu. yanzu ni babbar matsalata hanyar samu na yaragu ne kusan 90% kaga akwana atashi duk kudaden da muka tara daga ni har 'yan uwana karewa zasuyi. Gaskiya kuma kana gani banda motoci babu wani abinda muka mallaka. Ko gida bamu sayaba karshe idan mukayi wasa zamu iya komawa halin da muke ciki abaya. Meyasa kake tunanin hakan Awwal yafadi haka yayinda yake bude kofar shigowa dakin bisa dukkan alamu yaji dukkan zantukan dasukeyi. Rilwan yadanyi murmushin takaici tareda harara kana nufin bakasan dalilin da yasa nayi furucin nan ba? Ahankali awwal yakaraso kusa dashi yazauna sannan yace wannan shine amfanin yin abu da shawarar mutane, kaga da ace ka sanar damu abinda kayima computer dincan da wallahi ko ya zaiyi bazamu kyalesa yatafi da ita ba. Amma sai ka 6oye mana gashi nan kagani yanda abin yakasance. Kaga ni duk ba wannan ba. Yanzu me abinyi? Rilwan yakatsesa tareda jefamai tambaya. Eh toh yanzu dai mafita daya ne kawai muci gaba da hakuri da kadan dinda muke samun ahankali ahankali zamu kai wani mataki wanda mu kanmu bamuyi tsammani ba. Hmmm haba Awwal wane mataki kake gani zamu kai nan gaba? Kasani fa bamuda kowa kuma bamuda wani gata sai Allah. Ka duba kagani kannenmu muka kyalesu awajen wasu mutane, sabida bamu da aikinyi. Mun fita nema Allah ya kaddara munsamu amma yanzu gashi abin yana neman kufcewa, yakamata ace munsan yanda zamu bulloma wannan lamarin dan gaskiya nikam yanzu natsani musiba irinta yunwa da talauci kuma bana tunanin nakoma cikinta. Awwal yayi ajiyar zuci sannan yace inaso kayi abu cikin nitsuwa yanzu kyanta dukanmu muhadu muyi shawara sannan muga wanne abu ne yadace muyi ayanzu? Uziboy yace kwarai kuwa hakane yakamata kam. Yanzu bari nakira Sagir inaga yana dakinsa ko? Awwal yace suna falo shida netmaye. Uziboy yadauki wayarsa yakira netmaye yace suzo shida sagir su samesu adakin Rilwan. Bayan sunzo Uzairu yayi musu bayani sannnan yace ko sunada shawarar da zasu bayar ? sagir yace Allah ya kyauta ni atunani na gaskiya Rilwan gara kaje ka sami sadauki kafada masa gaskiyar zance idan akayi sa'a ya hakura kaga sai kucigaba da harka dashi. Netmaye yace ina sam haka bazai yiwu ba. Tunda kuka hanamu kar6an computer din ai yariga da yatafi dashi kuma idan yaji dadinta bazai yadda arabashi da ita ba. Hmmmm Rilwan yace yawwa natuna uziboy akwai wata matar da muka ta6a zuwa wajenta dakai wacce tace zanyi azumi na sati biyu sannan bazanje ko ina ba ina daki. Uziboy yadanyi murmushi tareda fadin kaji dan banza ba dacan kace kana da ulcer ba shiyasa kai bazaka iya yin azumi sati 2 babu lada ba, kodai ulcer din ta warkene? Rilwan yace kaji fa aini ko azumin shekara ne zanyi matukar masifar talauci bazata sake ra6ar inda nake ba. Awwal yace toh sai fa kabi duniyar ahankali karta kaika ga halaka. Rilwan yace karta kaimu dai duka, inacewa nidaku duk dayane komai nasamu bana warewa duka namu ne. Sagir yace Hakane yanzu abinda za'ayi sai kuje wajen matar tabaku nata taimakon. Rilwan yace hmmmm yanzu uziboy zamuje gobe ko? Uzairu ya amsa da cewa eh toh babu damuwa amma dan Allah idan kasan bazaka iya ba karka fara zuwa, domin kuwa wancan lokacin ma damukaje kaki komawa abin yabani Haushi ni kunyarta nakeji.. yi hakuri uzairu nasan banyi daidai ba. Uzairu yace bamatsala sai goben idan Allah yakaimu zamuje. Nan suka shiga hira tsakaninsu na tsawon lokaci kadan Rilwan yace yawwa dazu munyi magana da Khairat itama ta barni cikin tunani. Sagir yadubesa kamanya tabarka cikin tunani? Nanfa yasanar dasu yadda hirarsu yakasance da Khairat tace tana neman wani alfarma amma bata fada masa ko alfarmar me ba. Awwal yatuntsire da dariya kodai so take tace tana sonka ne? Rilwan yace kaga dakata haka kawai daga sanarma zance zaka kawomin zancen bala'i nifa bakasan natsani zancen soyayya yanzu ba? Haba sabida me katsani soyayya netmaye yajefa masa tambaya? sagir yace kuma kunsani ai, zulibaby masoyiyarsa ce ta jawo sadauki yakwace computer dinsa . Shegiya ba !, Rilwan yafada ransa a6ace, jiyayi gabadayansu sun tuntsire da dariya. Wato dariya ma nabaku ko? Kwarai ma kuwa kagani kanaso nahada ku da ita kuma yanzu kace katsaneta sam bazaiyiwu ba netmaye yabashi amsa, toh sai kaje kadawo da ita kagani yanda zan koya mata hankali shegiya mara kunya, ni Allah yakiyayeni ma ahakan wai ban aikata alfasha da ita ba, na hadu da wannan jarabawar da kuma na aikata wata kila mutuwa zanyi. Suka kuma tuntsirewa da dariya. Washe gari dasafe suka Shirya kai tsaye Rilwan da Uziboy sai gidan wancan matar, bayan sun gaisa tadubesu sannan tace sai yau kuka waiwayo? Uzairu yadan sosai kai eh wallahi kuwa sai yau muka sami daman zuwa. Sai tace sannunku da isowa takawo musu tabarma suka zauna sannan ta tunatarwa Rilwan duk abinda ta fada masa abaya. Azuciyarsa jiyake kamar bazai iya ba amma idan yatuna damuwar da zai iya shiga ta talauci gara kawai yatsa ayi masa. Dole ne ka kasance mai kauracewa dukkan zunubi. Sabida hakane ma yasa zakayi azumi har na tsawo mako 2 sannan anan zaka zauna agidana kayi bazakaje ko ina ba har zuwa kwanaki 14 su cika kafin nan insallameka. Rilwan yayi ajiyar zuci sannan yace toh mama zanyi iya bakin k okarina. Sannan tacigaba da cewa akwai dakunan baki zan hadaka da 'yata zata kaika dakin dazaka sauka. Sannan kuma ita zata rika kawoma abinci ako dayaushe sabida ba'a bukatar ka fita waje neman wani abu. Yace toh ina godiya mama. Sannan tace idan ka amince zaka iya tafiya kaje kadawo da kayan kinka yau ko gobe idan yaso sai ka fara. Yace toh na amince mama yanzu zankoma in debo kayaki ayau. Tace toh awancan lokacinma haka kace kuma tunda katafi ba labari ina fatan yanzu ba haka zakayi min ba? Yace zan dawo mama sabida idan bandawo kaina na cutai. Tace toh yanzu bari aje dakai dakin dazaka zauna anuna maka idan yaso idan ka dauko kayanka sai kaje kai tsaye ka ajiye. Yace toh. Ta daga murya tareda kiran sunan 'yar tata zeenatu,zeenatu sau biyu takira sannan wata tsiriryar murya ta amsa daga cikin daki tafito. Rilwan da Uzairu suka maida kallonsu zuwa inda muryar yafito. Wata 'yar matashiyar budurwa ce tafito daga cikin dakin sanye take da wani karamin riga wanda ya matse jikinta tareda wandon jeans darkblue kanta abude batareda ta saka dankwali ba tafito, tareda fadin mama ganinan takaraso wajen mahaifiyarta ta kalleta sannan taje jekisa dankwali kizo kikai wadannan masaukin baki. Ta juya takallesu sannan ta amsa toh takoma tasaka dankwali wani dauri tayi shi bairufe gashin duka ba sannan kuma gashinan dan kwalin asaman kayi, tayi wani turoshi gaban goshi. Tafito da wasu makullai ahannunta. Ta dubesu cikin sakin fuska muje nakaiku ko? Suka amsa toh. Sun tashi zasu tafi uzairu yace mama ina da tambaya tace inajinka. Yace idan yafara azumin shin zan iya kawo masa ziyara. Tace a'a bazaiyiwu ba sai yagama. Uzyboy yace ok. Suka kama hanya kasancewar gidan babban gida ne kuma yakasance babu kowa sai matar da kuma 'yarta kafin su iso 6angaren baki akwai dan tazara zeenatu na tafiya suna biye da ita abaya, tana tafiya tana wani juyi cikin kasaita har wani girgiza takeyi, Uziboy ya lura da ita sai yadan ta6a Rilwan ahankali yace masa kalura da tafiyar yarinyar nan kuwa? Rilwan yakalla sannan yayi ajiyar zuci kut lalle kuwa wannan yarinyar ta daukemu 'yan iska ko? Uzairu yace ah toh dama 'yan meye ne mu? Rilwan yace kaga idan kai dan iskane toh ni ba haka nakeba kaima tsaban sa'ido har idanunka yaje inda baidace dashi ba. Suka tsaya sa'insa ta danyi gaba sannan tajuyo tareda yimusu magana yaya dai kuke tsayawa muje mana. Dasauri suka kara hanzari har suka iso wani daki sannan yarinyar taciro makullin tabude tashiga tace ga dakinnan wannan shine dakin da zaku zauna, Rilwan yace mungode malama ya sunanki? Tadanyi murmushi sunana zeenat. Toh muna godiya zeenat. Sai takuma yin murmushi tareda mika ma Rilwan makullin dakin sannan tace kuhuta lafiya tajuya tafita takama hanya suka bita da kallo takuma sauya salon wani irin tafiyar wanda idan tayi taku ko ta ina na 6angaren jikinta sai ya motsa. Kamar tasan suna kallonta sai ta kuma juyowa suka hada idanu da sauri suka kauda kai kamar basu ba, tadanyi murmushi sannan tawuce ta tafi. Uzairu yadubi Rilwan tareda fadin kai bross anya kuwa zaka iya yin azuminnan tareda wannan yarinyar acikin gidan nan.? Yadanyi murmushi sannan yace hakan take.ls / HAKAN TAKE part 25 HAKAN TAKE part 25 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 18:28 Rilwan yadanyi murmushi sannan yadubi uzairu tareda fadin haba bross ai ko mayyace ita nan gani nan bari bata isa ta ruguza min shiri ba. Uziboy yayi dariya sannann yace lalle kuwa yaro bakasan sharrin mata bane. Rilwan yace sharrin mata yawuce abinda zulibaby tajawomin? Uzairu yace me ma zuli tayimaka? Ai wallahi bakaga komai ba. Rilwan yadanyi dariya sannan yace mutafi naje na debo kayakina din. Suka fita tareda kama hanya. Bayan sun dawo Rilwan yafada masu awwal yadda sukayi da matar sannan yace musu zai tafi sai bayan kwanaki 14 zai gama. Sagir yace wai nikam Rilwan wannan wane irin azumi ne? Ah azumi mana wane irin azumi daman kake tunani?Rilwan yabashi amsa Sagir yace ni naji kunce zakayi sati 2 acan sannan kuma babu inda zakaje sai acan.? Uzairu yataresa da amsar tambayar dalilin dayasa bazai fita ba sabida idan yafita yawo zai aikata zunubi kasan mutumin naka ai sai ahankali. Rilwan yadanyi dariya ai ni nafika takuruwa sagir kawai hakuri zamuyi zuwa sati biyun kafin komai yagyaru.. Sagir yace toh amma kuma gani nayi matar nan fa da kukaje wajenta kamar 'yar tsubbe tsubbe ce kamar bokace sannan kuma wane azumi ne zata cema kayi. Ba farilla ba nafila ba? Shin kuma idan kayi hakan waye zai baka ladar azumin? Uzairu yace ma Sagir kaga dan Allah kaikam wane irin mutum ne ace maka azumin wanke zunubi zaiyi sannan kuma ina ruwanka ko zai samu lada ko bazai samu ba me ruwanka? Sagir yace kaga Uziboy ya haka ne kam wannan fa dan uwana ne tun kafin yahadu dakai ya kuma inayi masa tambaya kana hanashi yabani amsa ? Toh ko kashin awaki ne ku ba 'yan uwa ba nafada din wai kai so kake yafasa zuwa? Rilwan yace jimana kudena cecekuce akan wannan batun. Sagir zaka ga amfanin wannan abin idan nagama kaji? Sagir yayi ajiyar zuci sannan yace toh ya taimakemu duka. Suka amsa ameeeen Rilwan yatattari kayakinsa yatafi dasu. Yaje gidan kai tsaye yabude dakin yashiga sannan yashirya kayansa acikin bayan ya gama yafito. Sannna yakulle dakin yanufi waje yana tafiya yaji ance bawan Allah dan tsaya mana, yawaiga yakalleta zeenat yafada sannan yadanja lumfashi yana jira yaji me zata ce masa, takaraso inda yake dakyau yanzu ta canja dressing kayan data saka yayi matukar yimata kyau. Barka dai kadawo ne? Ya amsa da cewa eh takuma jefa mai wani tambayar ina dayan abokin ka din? Yace mata ai ni kadai ne zanyi shi dan rakiya ne dama. Tace toh abin yayi kyau yanzu ina zakaje? Yace zan dan fita ne nayo shopping sannan nadawo yanzu, tace masa toh idan ba damuwa bari nayi maka rakiya mana? Yadanyi ajiyar zuci sannan yace ba matsala. Suka je har wajen da ya ajiye motarsa basu tsaya ko ina ba sai shopping suka shiga yace ko kinason wani abu ne? Tace a'a yace toh ba damuwa amma yakamata kidauki wani abu koda chingam ne. Tadanyi murmushi sannan tace idan nace zan sayi wani abu zanyi maka 6arnar kudi ne shiyasa. Rilwan yakalleta cikin mamaki sannan yace jeki dauka ko menene zan biya kudin. Tace a'a fa ? Yace ai ni na fadamiki? Tace toh sannan tawuce taje ta debo wasu man shafawa da wasu turare takawo ta ajiye shiko yashiga yadebo drinks da biscuit carbin da sauransu yacika kwando da kayaki sannan yaje sukayi lissafi. Yabiya musu kudin yadauki kayan har zuwa wajen da yayi parkin din motarsa sannan yasaka boot din motarsa yarufe daga bisani suka shiga motar suka koma gida. Suka sauka yaje yabude boot din tazo takama mishi suka saukar da kayan zai dauka tace no ka kyale kawai nasan kagaji sabida haka yakamata ka huta kafin yace wani abu ta dauka ta aza ledar kayan akanta sannan tanufi dakinsa din yana cewa kibari nadauka kayan akwai nauyi fa? Tace kyale kawai ance maka banida karfine, alokacin saiga mamarta ta fito hannunta rike da tsintsiya zeenatu ke ina kikaje? Ta daka mata tsawa, abinda yabawa Rilwan mamaki ko dar zeenat batayiba balle ta nuna alamun cewa taji tsoron tsawarda mahaifiyarta tayi mata din. Tadan sauke murya tareda fadin na rakashi ne yaje shopping. Tajuya takalli Rilwan kunya yakamashi sannnan yasaukar da kansa tareda fadin ayimaka afuwa mama bazata sake ba. Mamar tadanyi ajiyar zuci sannan Tace shara fa nacetayi min shine tafita kamar wacce zatayi dagaske daga baya na nemeta narasa, Rilwan yadanyi murmushi sannan yakuma cewa ayi hakuri mama. Yakarisa wajen zeenat yace haba ke kuwa zeenat haka akeyi ne abaki aiki saiki kyale sannan kuma kice zakiyi min rakiya? Dan Allah karki sake yin haka yanzu bani kayan bari in karisa dasu, mama tace bari takaimakasu kawai. Rilwan a'a mama gara takarbeki ai, mamar tace Allah ka kyale kawai bari takaima. Haka Rilwan yabari takaimasa har cikin dakin ta ajiye sannan taciro mayuka da turaren daya sayamata tace ya ajiye mata zata zo tadauka kar mamarta tagani shidai baice komai ba sai toh, tafita, takyalesa awajen yakwanta yamike akan gado yana hutawa sai yaji wayarsa tana ringing yadauka sai yaga Khairat yace madallah sannan yakara akunnensa tareda sallama. Ta amsa sannan yace lalle kuwa Khairat kin kware wajen iya saka mutum cikin zullumi, tace meyafaru yace kince akwai alfarmar da kikeso zaki nema awajenmu. Tace au haka fa kaga ni har ma namanta ma kayi hakuri. Rilwan yadanyi ajiyar zuci sannan yace toh naji nayi hakuri alfarmar me kike nema awajenmu? Ta kumayin ajiya zuci sannan tace yanzu muka gama waya da Awwal shin baka kusa da shine? Yace eh bama kusa kedai kisanar min kawai, tace dama bawani abu bane so nake kusani cewa yanzu haka soyayya ta kullu tsakanin Aisha da Hamma Sani amatsayinku na yayunta yadace ace kuna da labari ko? Rilwan yadanyi shiru yana tunani tareda zancen zuci Sani kuma yakeson Aisha? Hello Ya naji kayi shiru ne ta katseshi daga tunanin dayakeyi, dasauri yafurta zancen eh toh lalle kuwa tabbas naji dadin wannan zancen, sannan kuma babu abinda zamu iya cewa saidai Allah yasanya alheri . tace yawwa haka nakeson ji Allah yabar zumunci Rilwan yace ameeeen, saura ke muna jira aturo mana sako da sunan saurayin da yakesonki kema ko?. Saida gabanta yafadi shima adaidai lokacin jiyayi kawai ya furta zancen, tadanyi dariya sannan tace karka damu zakaji, yace toh ina jira ina labarin kawarki zainab? Tace ayya tana nan lafiya saidai tunda muka gama rubuta jarabawarmu ta karshe ma bansake kaimata ziyaraba haka itama bata ziyarceni ko sau daya ba. Rilwan yace toh idan kuka gana da ita kice Awwal yana gaisheta, tadanyi murmushi toh zataji insha Allahu Rilwan yace yawwa madallah nagode Khairat Allah yasanya alheri, tace ameeen sannan yakashe kiran tareda yin ajiyar zuci, bai lura dacewa akwai wanda yashigo dakin ba, kawai yadauki wayarsa yakira Sagir yana shiga yadauka hello yane bross, Rilwan yace akwai fa? Meke faruwa ne ? Sagir yatambaya, Rilwan yace wallahi akwai shin kuna tareda Awwal ne? Eh muna taredashi yabashi amsa , yawwa toh saka wayarka a free hand muyi magana duka, sagir yasaka sannan Rilwan yakira sunan awwal tareda tambayarsa shin kunyi waya da Khairat yanzunnan? Awwal ya amsa eh tabbas yanzu muka gama waya da ita, wane zance tafada maka? Kai tsaye yafadi zancen sannan Rilwan yace eh nima takira ta sanarmin amma yanzu yakuke ganin lamarin? Awwal yace kai nifa nace mata toh ne fa kawai sabida mutuncin dake tsakaninmu da ita, amma ni abinda baku sani ba zan fada muku gaskiya inji hausawa ranar wanka ba'a boye cibi toh zancen gaskiya nadade ina son Aisha acikin zuciyata. Sagir yayi ajiyar zuci sannan yace hmm kaima kenan ai nima tuni nakeda wannan kudirin, gaskiya nima bazan 6oye muku ba akwai son Aisha acikin zuciyata tuntuni kawai kyalewa nayi har zuwa lokacin da zata girma kafin nan in bayyana mata, Rilwan yace look dan Allah ku tsaya excuse me yakamata muyi maganar fahimtar juna daku kungane domin nasanku wani lokaci lamarinku sai ahankali yanzu zaku iya samun matsala kan wannan batun toh bari nagaya muku nima kaina da kuke gani inada wannan kudirin kwatankwacin nakun kawai ban ta6a sanar muku bane amma dan Allah inaso tunda dukan mu munasonta yakamata ace muhadu dukanmu muyi hakuri mu rufawa juna asiri mubawa Sani hadin kai domin kuwa shine mafi cancanta ya Aureta, basai nayi muku karin bayani ba nasan zaku fahimta. Awwal yace malam dakayi mana karin bayanin zaifi dacewa, Rilwan yace idan muka nace muna sonta yanzu acikinmu waye zai janyewa wani? Shin acikinmu muna da tabbacin cewa zata so waninmu ne? Ayanzu haka zancen da ake tana sonshi yana sonta sabida haka kaga shiga karaba tsakanin masoya abune mai matukar wahala sabida haka gara muyi hakurin ina ga shine mafi alheri agaremu baki daya. Sagir yayi ajiya zuci sannan yace ba ga irinta nan ba shiyasa ni tun farko banso zaman yarinyar nan agidancan ba, da agidan lauwali tazauna da ina haka zai faru? Sai kuma kayi nikam dai nafada muku Rilwan yakashe kiran ransa cike da haushi juyawar dazaiyi sukayi idanu 2 da zeenat tana zaune akan kujeran dake cikin dakin, tana shan ruwan lemun daya saya, yabita da kallo cike da mamaki sannan yace yaushe kika shigo? Tadanyi murmushi sannan tace wacece Aisha danaji kuna zancenta awaya? Baiyi mamakin tambayarta dinba sabida yasan taji dukkan maganar dayakeyi shiyasa ta tambaya., budan bakinsa sai yace mata HAKAN TAKE / HAKAN TAKE part 26 HAKAN TAKE part 26 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 18:29 yacemata kanwata ce me dalilin wannan tambayar, tadan zum6ura baki sannan tace babu kawai natambaya ne, yace ok toh amma meyasa kikashigomin daki kai tsaye batareda kinyi min sallama ba? Zeenat tace kayi hakuri malam nazo shan ruwan lemu ne kuma dazaran nagama zan fita nabarma daki tunda korata zakayi. Rilwan yace toh nidai tambayarki nayi. Tace toh jirani nashanye wannan goran juce din zan baka amsa. Yace toh sannan ya tashi yabude jakarsa yafitar da computer dinsa yabude yashiga net, yamanta da ita. Har tagama shan juce din ta tashi tatafi. Kafin nan yasami nitsuwa. Can da yamma bayan sallar isha'i tashigo dakin tareda yimasa sallama. Har alokacin yana kan computer ya amsa batareda ya kalli inda take ba, wannan wane irin mayen computer ne ? Azuciyarta ta fada sannan takariso sannan ta ajiye abincin daga bisani tazauna akan gadonsa tareda fadin ga abincin na kawo ma, ko kallonta baiyi ba sannan yace toh naji tunda kin ajiye ai sai ki tafi. Tace au yanzu dinma korata zakayi ko? Yace bakoranki zanyo ba, banaso wani abu yafaru ne? Me kenan kake tunanin zai faru tafada yayinda tatashi tsaye tarike kunkumi, .ahankali ya rufe computar dake gabansa daga bisani yatashi shima yatsaya yana kallonta, kinga nasan kin fahimci ko me nake nufi sabida haka ni da zaki dena zuwa dakin nanma da kintaimakeni. Tace toh yayi kyau namiji kazo kasameni agidanmu kuma kace kar na shigo wannan dakin? Ai wallahi baka isa ba, yadan saukar da murya haba zeenat bahaka nake nufi ba, bana so mahaifiyarki tashiga cikin zargina bisa aikata alfasha dake shiyasa kinga nazo neman taimako ne kuma ta taimakamin harda wajen zama kuma kinsani gobe zantashi da azumi sabida haka ni banaso wani abu yazo yafaru atsakaninmu yadakata da zancensa anan. Tadubesa sannan tace kagama bayanin naka? Toh bari na fadamaka wani abu karkayi tunani cewa zaka sameni ayadda kake tunani ni kawai zuwa nake ziyartarka sabida naga kana cikin kadaici sannan nima kadaicin nake fama da ita. Sannan kuma ni haka nake duk wani bako idan yazo gidannan sai na saba da shi toh me kake tunani? Abinda zan fadamaka kawai shine ka kwantar da hankalinka mahaifiyata bazata zargeka da komai ba. Sabida bayau aka fara kawo baki nake zuwa wajensu na dauki lokaci mai tsawo ba amma tunda kanuna bakaso shikenan dazarar nakawo maka abinci zan tashi intafi. Jikinsa ya mutu sannan yace toh kiyi hakuri kar ranki ya6aci ni ina gudun sharrin shaidan ne, amma tunda kika furta haka toh shikenan, yakaraso yadauki abincin yabude wow yafada yayinda wani kamshi yadoki hancinsa yawu taru a makogoronsa ya hadiye da kyar sannan yace daga kallon wannan abincin Mamace ta girka shi ko? Kamar bataji yayi magana ba ta manna masa hauka ya waiga yakalleta fuskarta ahade bisa dukkan alamu akwai abinda ya sosa mata rai, gani yayi ta tashi kai tsaye taje tahau kan gado tareda bude computer dinsa, ke me hakan bakya gani ne sai wani dale min kan gado kikeyi? Tajuyo ahankali ta waigo kanta bisa dukkan alamu tasaki fuskarta awannan karon tacemai ya akayi kai wallahi kacika korafi dayawa angayamaka ban iya aiki da computer bane, dadin girkin dayakeci shiyasa bai damu sosai bisa ta6a masa computer datayi ba,dukda kasancewar yatsani yakalli mace tana aiki da computer musamman tunda zulibaby ta jaza masa 6araka, murmushi yadan saka wanda bai iso zuciya ba sannan yace sai kace wata kwararriya. Tace hmmm baka sanni bane nifa ba'ayimin magana matukar nahau kan computer ina aiki, ke din? Tace kwarai ma kuwa, yadanyi shiru tabbas acikin abokan huldansa akwai wanda yake yawan irin wannnan furucin amma kuma nan take yamanta ko wanene, sai kawai yarika maimaita jumlar acikin kwanyarsa, nifa ba'ayimin magana matukar nahau kan computer ina aiki ya maimaita zancen kusan sau 5 kafin yatuna da cewa tabbas oga sadauki shike irin wannan furucin cikin hanzari yakatse tunaninsa tareda fadin zeeenat kenan waye yakoyamiki aiki da computer wanda idan har kina kai baza'ayi miki magana ba? Budan bakinta tace masa ina ruwanka? Yadanyi shiru sannna yasaukar da kansa gaskiya fa wannan yarinyar akwai alamu itama jace cikin kankanin lokaci Rilwan yaji tafara birgesa sabida shi mutum ne maison arinka challenging dinsa, . Har yagama cinye abincin tana ta faman latse latsen computer. Sannan yatashi tareda yin hamdalah yanufo inda take domin yaganewa idanunsa me takeyi ne a computer dinnan. Yana zuwa yakalli tana ganin wani film din chinese batareda ta kunna volume ba, yace mata nagama sai kije kidauki kwanukanki kije ko? Tace toh bari wannan film din yakare yace sam bazaiyiwu ba zata karar masa da caji kuma gashi yanzu babu nepa, sukayita sa'insa har tagaji ta tashi tattare kwanukanta sannan tace masa for the next time idan kaganni akan computer kar kayimin maga saina gama, yace toh naji jeki kya gaisheda mama. Rilwan yarufe computer dinsa tareda cire rigar dake jikinsa daga bisani yamike akan gado tareda jan dogon lumfashi yanata sake saken zuci duk lamarin duniya yabiya damesa sai yaji takuma shigowa, me kuma kika dawoyi? Tace mamana ce tace in kiraka yace toh jeki ce mata ina zuwa, tajuya tafita sannan yadauki rigarsa yasaka yakuma biyota abaya. Bayan ya iso yazauna yagaisheta ta amsa sannan tafara yimasa bayani kamar haka: kayi hakuri kadanne zuciyarka zaka sami biyan bukata kaji? Karka dauka cewa wannan azumin daban yake da sauran azumi. Kamar yadda kakeyin kowanne azumi haka zakyi wannan kaji? Yace mata toh maman zeenat in Allah yaso ya yadda baza'a sami matsala ba. Tace toh haka nake fata zaka iya tafiya. Yayi godiya sannan yatashi ya koma dakii. Yadauki wayarsa yahau whatsAp alokacin Awwal yana online suka fara chatting jim kadan Sagir ma yahau sai suka hada group suka fara tattaunawa, sagir yace yanzu yakuke ganin zamu fuskanci wannan zancen? Rilwan yace ai zance yakare sai dai kawai mukai musu ziyara, kamanya kake fadin ziyara ne nifa bazan hakura ba sai dai idan Aisha ce ta furtamin cewa bata sona Awwal yaturo message din cikin zafin rai, Rilwan yace kaga Awwal ko kaki Allah dolen kane kayi hakuri , kasani fa matar mutum kabarinsa, wani baya ta6a aurar wani koda ace kun taso kuna soyayya da ita idan Allah bai nufa ba bazaka ta6a samunta ba. Awwal yayi ajiyar zuci sannan ya rubuta hmm nasan da wannan amma ai akwai cancanta , Sagir yace haba Awwal meyasa kake tirjiya akan abinda kaima kasani baidace ba? So kake mukoma gidan Alhaji Haruna mu kwace kanwarmu bayan mun riga da mun damka masu ita amana sun riketa har tazama cikakkiyar mace, da wane idanu zamu fuskancesu da wannan zancen, Rilwan yace Awwal zance yakare komai yawuce Aisha dai dole muhakura da ita garama kacireta aranka. Haba nasani bazaku fahimta bane, son danakeyiwa Aisha yazarce yanda kuke tunani abu ne wanda bazan iya misalta adadinsa acikin zuciyata ba koda zan hakura na tabbata zansha wahala kafin na horar da zuciyata. Kayi tunani Awwal karka bamu kunya Rilwan yafada. sagir yace yakamata muje mudubasu ma muga yanda suke. Rilwan yace kwarai kuwa gaskiya yakamata muje amma bari idan nafito mun daidaita harkarmu saimuje mudubasu. Sagir yace bamatsala alokacin Awwal yasauka sannan yarufe data dinsa zuciyarsa cike da damuwa ya kwanta bacci yabarsu a group din. Suka cigaba da tattaunawa har karfe 12 na dare sannan suka sauka daga whatsAp din, da asuba misalin karfe 3 Rilwan yaji ana kwankwasa mishi kofa yatashi yabude yakalli maman zeenat takawo masa abinci gashi abincin sahur dinka yakar6a tareda yimata godiya. gari yawaye yakwanta bacci har shine bai farka ba har karfe 11 na rana bayan yatashi ya jikinsa duk yayi nauyi alokacin yunwa tafara mazgarsa yau fa za'ayita wallahi azumin nan yana garani yafada azuciyarsa. Yatashi yayi mika sannan yafita ya kuskure bakinsa yadawo dakin yazauna. Gaskiya zan wahala kafin nafita daga wannan gidan haba sai kace prison. Daga bakin kofa sai daki hmmm gaskiya neman abin duniya da wuya yake. Ringing din waya ceta takatsesa daga tunanin dayakeyi yajuya yakalla sai kuma yaga ba wayarsa bace. Ahankali yasaka hannu yadauka ba mamaki wayar zeenatu ce toh amma yaushe kuma ta shigo dakin nan bansani ba? Hmmm My SADAUKI sunan dayagani anyi saving din lambar kenan. Kai wannan kuma wane sadauki ne? Har wayar yagama ringing yana juyata yana kallo sannan yaduba lambar sai yaga yasha bamban lambar dayake tunani. Yayi ajiyar zuci sannan ya ajiye wayar awajenda yakalla. Sai yatsinci kanshi yana damuwa bisa sunan da yaga ta rubuta akan lambar da aka kirata dashi basai ansanar masa ba yasan wanda yakira bazai wuce saurayinta ba, da sauri yakatse tunaninsa da cewa toh ina ruwana ma da saurayinta wannan ba abinda yashafeni bane sabida haka garama nadena tunawa,dukda haka abin yaki yadena kaiwa da kawowa acikin ransa. Sallamar datayi ya maida hankalinsa zuwa inda take sannan ya amsa mata. Tace kafarka kenan? Ya amsa mata da cewa eh , tace namanta wayata shiyasa nazo dauka yace toh gashi nan kinada missed called tace waye. Yace nidai naga an rubuta My sadauki akan lambar, tadanyi murmushi ok sannan tadauki wayar cikin zumudi ta kama hanya zata fita yace tsaya mana zeenat waye kuma kikayi saving lambarsa haka? Tace ina ruwanka tamaida masa martani? Ajiyar zuci yayi sannan yabata amsa cikin hanzari akwai ruwana din wallahi sai kin bani amsa kafin ki fita daga dakin nan, haba Rilwan kamanta kana azumi ne? Ina ruwanki da azumin dana keyi? tadan saki dariya sannan tace me ya gameka dashi saurayina ne, yace saurayi? Tace kwarai kuwa sannan yace yayi kyau Allah yabarku tare. Tayi murmushi tareda cewa ameeen nagode. Sannnan tafita yabita da kallo hmm da kyau wannan har zumudi take? Yakoma yazauna ana haka yayi kwanaki 10 yana azumi yanzu kam yariga da yasaba da lamarin kullum shakuwa sukeyi shida zeenat. aranar dayake da azumi na 13 yana kwance yana rike da waya tashigo tareda yin sallama ya amsa mata takariso jikinta babu karfi tazauna akan gadonsa yadaga kai yakalleta fuskarta ahade. Lafiya kuwa zeenat? Tace lafiya lau yanzu idan kagama azumi shikenan zaka tafi? Rilwan yayi ajiyar zuci sannan yace kwarai kuwa tafiya zanyi dan wallahi yanzu haka jinakeyi kamar wanda yayi shekara agidan yari. Takara hada fuska sannan tace gaskiya idan katafi bazanji dadin zama ba acikin gidan nan. Yace sabida me kikace haka? Cikin shagwa6a tace sabida shakuwar da mukayi. Yace karki damu ni zan rika kawo muku ziyara ako wane sati. Tace hmmm shikenan kaduba fa tunda kazo gidan kullum ina zuwa wajenka samada 5 amma kai kace a sati sau 1 kawai zaka ziyarcemu? Yakuma yin ajiyar zuci sannan yakalleta zeenat wato akwai wani abu dayake birgeni dake, tadubesa cikin hanzari me kenan tajefa masa tambaya, yace idan kika hada fuska kinfi kyau. Alokacin saita dan saki murmushi sannan yakuma cewa, nasake lura da wani abu kuma idan kina murmushi kyanki yana ninkawa. Sai kawai ta kece da dariya sai yakuma cewa idan kina dariya kuma.. Dakata dan Allah karka sa ciki na yayi ciwo tafada yayinda takatseshi sannan tamike akan gadonsa tace bari na huta, haba muna tadi zaki katse mana zance ko? tace eh nafahimceka ai wato sabida nashigo jiki na amace shine kakeso kaga inata dariya ko? Yace hmmm kwarai kuwa gaskiya banason ganin 6acin ranki, tace toh takwanta yajuyo yakalleta dasauri yakauda idanunsa sabida kar azuminsa yasami matsala yadda yaganta. Dan Allah kinga kitashi kizauna banason ganinki ahaka karki jawomin asarar azumi. Tace toh me aciki azumin da kagama. Yace saura 2 ne fa tace hmmm karka damu biyun nan ba dole bane nida zakabi tawa ma da ka dena wahalar da kanka ma. Domin kuwa mutane dayawa sunyi azumin nan babu wanda yata6a dadewa har na kwanaki 14 sai kai. Hmmm ai kowa da irin bukatar dayake nema. Tace hakane amma wace bukata kake nema kai? Rilwan yace ina ruwanki? Tace kaga dan Allah kadena irin haka kai dazarar natambayeka amsarka bata wuce ina ruwanki? Rilwan yayi dariya sannan yace ai kece kika fara sabida haka ni bazan baki amsa ba, tace toh bari kagani ahankali tataso tazauna akusa dashi ya kalleta kyan surar jikinta yakara bayyana akan idanunsa dasauri yakauda idanunsa. yace mata me hakan? Tace ina ruwanka? Haba kinmanta ina azumi ne? Takuma cewa ina ruwana? Yatashi yamatsa takuma matsowa yace dan Allah kidena mana tace toh amsamin tambayata. Cikin kosawa yace mata ni 6arawo ne shikenan. Ta kyalkale da dariya sannan ta tashi takalli tsakiyar idanunsa, uhmmm kaiba 6arawo bane. Yace waye yafadamiki haka tace kawo hannunka mugani. Yace sabida me zan baki hannu na? Zeenat tace oh my God kaikam wane irin mutum ne, tamika hannu ta cafke hannunsa tarikeyatsunsa ta warwaresu sannan tace yatsun mai rike bindiga baya 6ata. yafizge hannun yayi me haka kike ta6a min jiki? Tace au baka so mace ta ta6a jikinka ne? Kuma nakalli hotunanka da 'yan mata acikin computer dinka? Ke bakisan ina azumi bane kibari idan nagama azumi kema sai mu dauki hotunan dake. Tace rike hannu yana karya azumi ne yace mata bansani ba sabida ni ba malami bane. Bisa dukkan alamu ransa ya6aci . Tace haba Rilwan shikenan dan na rike hannunka sai ka6ata rai dani? Yace kinga abin da nake so dake ki ficemin daga cikin daki tun kafin ranki ya6aci tace kayi hakuri bansan ranka zai 6aci bane da bazan rike hannunka ba. Yace ni ba wai rike hannu na dakikayi ne ya dameni ba kawai kije nakeso. Idan yaso ranar da nagama azumin kyazo ko guntule hannun kiyi.HAKAN TAKE part 27 HAKAN TAKE part 27 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 18:31 tadanyi murmushi wanda baikarasa harcikin zuciyartaba sannan tace masa kayi alkawarin hakan? Yace mata yes i promise kije kawai idan nagama kyayi duk abinda zakiyi da hannun tace ok. Promise promise promise sau uku tamaimaita sannan tajuya tace zan maimaita maka wannan kalmar alokacin da kanemi karya alkawari. Yace mata ok toh naji ko ma me kifada nikam kije. Tawuce tafita adakin kafinnan hankalinsa yadawo jikinsa. Yazauna yayi shiru yana tunani hmmm ni meyasa ma ban wanketa da mari bane? Ko da yake gara danayi hakuri zata iya rusamin aiki. Kiran daya shigo wayarsa ne yakatsesa daga tunanin dayakey yaduba yakalli uziboy yadauka tareda sallama. Bisa dukkan alamu ba'a cikin hayyacinsa yake sosai ba akwai alamun ya cake. Rilwan yace ya akayi ne bross? Uziboy yace ka kyale kawai ya hutawarka? Rilwan yace wane hutu kuma kake tambaya ai ni tunda nazo nan gidan yanda kasan akan kaya haka nakeji. Uziboy yakyalkyale da dariya toh ina labarin mutumiyarka? Rilwan yace kuut ai wallahi yanzu dakyar na ku6uta daga sharrinta. Uziboy yadan saki dariya sannan yace ban fahimceka ba wane irin sharri kenan? Hmm kaima ai kasani yanzun nan takawo min farmaki Allah yakwaceni inata karanta falaki da nasi, hhhhhh uzairu ya kuma fecewa da dariya kaidin nan gara ne fa wallahi nikam nasani da ace nine da sai dai narinka karya azumi kullum, Rilwan yace nasani ai kai asalinka dama dan iskane amma ni ai kaima kasani banayi? Uzairu yace haba mene yashiga tsakaninka da zulibaby harta jawo maka 6araka. Rilwan yace wallahi babu kawai Allah ne ya jarrabeni ta 6angarenta, suka kama musu tsakaninsu Rilwan yagaji ya katse kiran daga bisani yakwanta bacci yadaukesa shine bai farkaba sai magariba yatashi yasami ankawo masa abinci an ajiye amma baiga kowa ba, yadan tsaya yatambayi kansa shin yau kuma zeenat ce takawomin abinci batareda ta tsaya ba? Lalle kuwa yau wannan abin yadan 6ata mata rai, ko da yake wannan ma zaiyiwu wani shiri takeson shiryamin. Ko ma menene bata isaba saura min rana 1 kawai, cikin hanzari yakatse tunaninsa sannan yakarisa yakwashi abincin da aka kawo masa din. Daga bisani yaje yayi sallah yakuma dawowa yakwanta yana chattin ta shigo ko magana batayi masa ba sannan ta dauki kwanukanta tajuya ta tafi Rilwan yabita da kallo taje kusan bakin kofa yace ke zeenat yanzu kuma ba magana ne? Ko kulashi batayiba tafita. Yatashi akan gadon yabiyota har bakin kofar yana kiran sunanta ta manna masa hauka, abin ya kular dashi yace idan bazaki yimin magana ba ko ashar ai saiki duromin. Abin yabata dariya amma duk da haka tajure sabida ta fahimci nunawa datake ta damu dashi shiyasa yake jamata aji. Yadawo cikin dakin atsarge. Hmmm bari tadawo wato dan taga yanzu nasha ruwa shiyasa ta manna min hauka ko sai kuma na dauki azumi kizo kibi ki fitine ni ko? Hmmm zanyi maganinki. Washe gari da asuba kamar yadda sukeyi kullum da asuba mahaifiyarta ce ke kawo masa abinci. Tazo da wani karamar buzu ta shimfida sannan tace yazauna sannan tayi masa wasu bayanai sosai kamar dai huduba ababen da zai kiyaye daga bisani taciro wani magani tayi masa hayaki dashi sannan ta tashi tace masa shikenan idan ka kai wannan azumin kagama akwai maganin da zan baka amma sai kaga dama zakayi amfani da ita bawai dole bane. Rilwan yadubeta mama shikuma wanne irin magani ne? Tace wani garin magani ne hade da kashin bayan wani tsuntsu wanda zaka yanka jikinka kasaka aciki duk wata masifa data shafi zamani kadauka cewa kawai ka tsallaketa. Rilwan yace eh toh mama inason wannan maganin amma bazan 6oye miki ba fa ina tsoron yanka jikina ballema har insaka wani magani. Tadanyi dariya Rilwan kenan karka damu ba lalle bane sai yanzu kuma bance dole ne sai kayi ba idan har kana ganin akwai damuwa zaka iya bari sai lokacinda kashirya sai kayi, Rilwan yace inaso zanyi amma ba yanzu ba. Tace yawwa dana haka nakeso naji kafada. Yanzu dai sai gobe bayan ka gama azumin kafin katafi zanbaka komai. Rilwan yayi godiya sannan tatashi ta tafi. Yau kam wuni yayi bai kalli zeenat ba, baisan dalili ba shidai kawai jinsa yayi abin yana matukar damunsa hmmm yau ta dauke kafa, haka ya wuni yana ta latse latsen waya da shige shige daga wannan shafin zuwa wancan shafin idan yagaji yakwanta ya kwashi bacci haka yakasance har zuwa lokacin da aka kira sallar magariba. Abindayabashi mamaki yau ba'a kawo masa abincin buda baki ba. Yafita yayi alwala sannan yadawo yayi sallah yabincika cikin kayayyakinsa yadauko biscuit carbin tareda juce yafara buda baki dashi alokacin sai ga zeenat tashigo dakin akaro na biyu batareda tayi sallama ba yadaga kai yakalleta sanye take da kayan hausawa atamfa mai launin pink kayan sunyi matukar yimata kyau. Ta kariso har zuwa inda yake sannan ta ajiye masa abincin batareda tace masa uffan ba tajuya zata tafi. Yace zeenat dakata inada magana dake. Ko juyawa batayi ba, tacigaba da tafiya, baisan ya akayiba jiyayi kawai yana sarrafa ga6o6in jikinsa yayinda yaje yarike hannunta, a ankare yake ita ko tamkar akufule take tajuyo masa da mari Allah yataimaka yayi gaggawan tare hannunta kafin ya karaso kan fuskarsa, yadan sauke muryarsa kasa kasa tareda fadin haba zeenat, yaushe muka fara haka dake yaushe muka fara gaba? Ki fadamin, haba zeenat dan na zauna agidanku na tsawon kwanaki 14 ace yau har anjikanmu nidake? Gaskiya abin baidace ba kiyi tunani dai zeenat idan laifi nayi miki ai saiki sanar dani, kaga kasakemin hannu na wallahi ko kuma in doka ihu yanzu mamana tazo kuma kasani duk zancen dana fadamata zata dauka, yadanyi shiru yana tunani, wani abu nakaiwa da kawowa acikin kwanyarsa, wani tunani yace shin wai menene atsakaninka da wannan yarinyar wanda har take neman tayimaka irin wannan cin mutuncin batareda kakosa ba. Yasake hannunta sannan yace bazanyi mamaki ba, nagode ma Allah daya nunamin afili ke abokiyar hamayyata ce, alokacin danake fama kina ta nemana ashe dama so kike ki rusamin tanadi ko? Wato yanzu kinga nagama batareda kinsamu biyar bukatarki ba shine zaki yanke igiyar mutunci dake tsakanina dake ko? Weldone zeenat kinyi daidai nagode nima Allah yabani abinda za'azo nema awajena. Taja tsaki tawuce shikuma Ransa a6ace yakoma cikin daki yazauna abin yabi yadamesa. Zancen zuci kawai yaketayi wannan yarinyar batasan ko ni waye bane shiyasa takemin irin wannan rashin kunyar amma kyaleta sai na koya mata hankali tukunna zata gane, wani tunanin kuma yakan saka masa shin me yayima wannan yarinyar ne? Dan tarike hannunsa yace tasake shikenan sai abu ya zama fada. Haka yakwana kusan baiyi bacci ba duk gidan yabi ya ishesa. A6angarentama bayan taje takwanta kalaman daya furta mata suka rika dawowa suna yawo acikin kwanyarta " nagodewa Allah dayanunamin cewa ke abokiyar hamayyata afili" "nima Allah yabani abinda za'azo nema awajena". "alokacin danake fama kinata nemana ashe dama so kike ki rusamin tanadi ko" sai ta wanzu tana dana sanin hada masa fuska datayi, sannan ta godewa Allah dayabashi ikon tare marin datakaimasa. Haka nan itama takasance daren cikin sake saken. Washe gari dasafe yagama hada kayakinsa sannan yatashi yaje yasami. Maman zeenat yagaisheta tareda sanarmata cewa yanaso zaitafi, haba malam Rilwan kabari gari yawaye mana yanzu karfe 6:30 ne fa nasafe? Yace inaso akwai aikinda nashirya zanyi ayau ne shiyasa nakeson tafiya. Tace toh amma yakamata kakoma daki kazauna kajira sai mungama breakfast idan yaso saikaje. Baiyimata musu ba yakoma yadauki wayarsa yahau internet jim kadan, sai ga zeenat takawo masa Abinci tashigo da sallama, yaki amsawa takaraso har wajen dayake ta ajiye masa abincin. Zatayi magana yadaga mata hannu alamun tayi shiru, hakan take sai takasa cewa komai sannan yadaga hannunsa yanayimata nuni da hanya taje kawai batareda yafurta mata wani zance ba. Batace komai ba tafita sannan ya dauki abincin yacinye, daga bisani yadauki jakarsa yafito sannan yakulle dakin yakyale makullin awajen. Sannan yanufi 6angaren Mahaifiyar zeenat, kai tsaye adaidai lokacin tayi bakuwa suna zaune akan taburma yasamesu yakarasa da sallama, tace yawwa kaga yanzu ka karya kumallo ai zakafi jin dadin tafiya. gashi kuma nayi bakuwa. Ya kalli bakuwar adaidai lokacin dasuka hada idanu da ita saida gabansa yafadi, hajiya fadila kuma anan gidan? Yatambayi zuciyarsa sannan yayi shiru itama data ganshi sai dataji wani faduwar gaba daga bisani tajure tace. Ah Rilwan ne anan. Yace eh hajiya nine, yau kece bakuwar tamu anan? Tace eh toh aini anan gidan ba bakuwa bace domin kuwa gidan kawata nazo. Yace ayya yayi kyau. Mahaifiyar zeenat tace dama kunsan juna ashe? Hajiya fadila tace ai wannan abokin wasu yan aiki na ne da can amma yanzu sun zama manya ko ziyara basa kawomin. Kaji wani zance awajen matarnan Rilwan yafada acikin zuciyarsa daga bisani yakatse tunaninsa yace Hajiya aikine yayi mana yawa amma idan muka sami lokaci zamu ziyarceki. Maman zeenat takatse musu zance dacewa tunda kace kana sauri bari na sallameka sai katafi. Rilwan yace toh, ta tashi tashiga ciki tabarsu tareda hajiya fadila. Rilwan yace Hajiya dama ashe ke kawar maman zeenat ce? Ta amsa dacewa eh ina su Awwal da sagir.? Suna lafiya lau yabata amsan. Nan Suka fara tadi. Alokacin saiga zeenat ta iso wajen ta durkusa tagaishe da hajiya fadila. Daga bisani taje tadauko wani kujera tazauna akai. Har maman zeenat tafito da wasu magunguna ahannunta tamikawa Rilwan sannan tayi masa bayani ta tunatar dashi yanda zaiyi amfani dasu, aduk lokacin dayake tunanin zai shiga wani hargitsi yaka iya amfani da maganin da ake yanka jiki azuba aciki. Sannan kuma tabashi wani hayaki wanda zai riqa amfani dashi. Ya kar6a yanata godiya sannan yatambayeta nawa zai biya bisa dukkan aikin da tayimasa? Tace yakawo kawai abinda yaga zai iya. Damin kudi yafitar dauri biyu yamika mata wanda kowane dauri guda naira dubu dari ne aciki. Sannan takar6a tareda fadin duka wannan kudin. Yace mata haba mama wannan ai kadan ne. Tace toh madallah Allah yasa aga alheri ya amsa ameen, sannan yace mama dan Allah inason wani alfarma kuma. Tace toh menene yafaru,? Yace zeenat ce bansan menayi mata ba take fushi dani yanzu haka maganar danake miki tun shekaran jiya bama magana da ita, koda nayi mata magana sai tayimin shiru bata bani amsa haka idan takaimin abinci haka zata ajiye batareda tayimin magana ba. Mama wannan abin yana matukar damuna shine nakeson a roketa idan ma laifi nayimata ta yafemin kafin nan intafi. Hajiya fadila ta kalli zeenat sannan takuma kallon Rilwan tace toh? Maman zeenat ta waiga takalli zeenat sannan tace ke zeenat haka akeyi? Me yafaru kika dena yimasa magana, Rilwan baita6a tunanin zeenat batada kunya ba sai a wannan lokacin domin kuwa kai tsaye ta furta zancen cikin shagwa6a. Mama fa cewa nayi ina sonsa shikuma yaki amincewa da tayin soyayyata. Wani irin suka yaji kamar ancakemasa kibiya akirjinsa yasaka hannu yadafe kirjin take yaji zufa na faman ketowa daga sassan jikinsa ga kuma kunya data ke naman mamayesa gabadaya bai iya cewa komai ba. Hajiya fadila ce tayi zance cikin raha tace,els / HAKAN TAKE part 28 HAKAN TAKE part 28 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 18:50 hajiya nabila tace toh wato dai ke wannan 'yar bakida kunya ko? agaban idanuna da mahaifiyarki ga kuma shi Rilwan din kikeyin irin wannan furucin? Zumbura baki tayi tareda juyawa. Mahaifiyarta tadaka mata tsawa tashi ki6acemin anan tun kafin ranki ya6aci. Ta tashi tana dan sam6atu cikin shagwa6a tawuce daki kai tsaye taje tafada kan gado tana zubarda kwalla. Shiko Rilwan jiyayi tamkar yatsaga kasa yashige sabida tsabar kunyar data kamashi. Yasaukar da kansa yayinda mahaifiyar zeenat tadubesa shin zancen data fada haka ne? Rilwan yadanyi shiru yana tunani, shidai a iya saninsa basu ta6a zancen soyayya da ita ba balle tace tanasonsa harma yaki amsawa, bakace komai ba? Takatsesa daga sake saken dayakeyi tareda fadin kayimagana mana Rilwan. Cikin hanzari yadago kansa yadubeta sannan yace mata haka ne tasanarmin tana sona haka nikuma nace bana sonta badan komaiba sabida banzo wannan gidan dan ita ko dan nayi soyayya da itaba.nazone bisa neman wata bukata ta mai matukar muhimmanci. Kinga ni idan na amince na amshi soyayyarta akan iya samun akasi bisa abinda nazo nema. Kwarai kuwa Rilwan kana da gaskiya gara da ka kaurace ma zancen soyayyar data kawo maka domin kuwa kasan mata tunaninmu kadan ne. hajiya fadila ta katsesa da zance. Yace Hajiya kenan yadan sosa keya bayason suhada idanu da mahaifiyar zeenat. Hajiya fadila tace toh yanzu kai din kana sonta ne ko dai... Dakata Hajiya karki takura masa, kaga Rilwan zaka iya tafiya. Yatashi tareda godiya yanufi inda ya ajiye motarsa, mahafiyar zeenat tadubi Hajiya fadila haba hajiya kina ganin gabadaya kunya yabi yakama yaro sai faman tambayarsa kikeyi. Kikyalesa kawai idan yana sonta shida kafafunsa zai tako yanemeta. Hajiya tace kwarai kuwa wannan zancen naki hakan take. Kinga wannan yaron idan har shine toh fa karkikawo tunanin zai yaudari 'yarki. idan har wannan ne zeenat dinki ta dace dashi toh lalle kuwa natayata da murna sabida mutum ne kamili. Mahaifiyar zeenat tace hmmm toh Allah yakyauta. Rilwan yakarisa rumfar dayayi parking din motarsa tun ranar dayazo gidan ya ajiyeta sai yau kwanaki 14 kenan. Yasami tayi kura tako ina sabida haka yasa yabude motar yaciro wani kyalle yabi yagoge jikin motar gabadaya hakan yasashi yadan 6ata lokaci. Daga bayan yagama yashiga motarsa yakama hanya shine bai tsayaba sai gidansu, yashiga yayi parking kai tsaye yawuce ciki. A falo yasamesu gabadaya suna buga wasan ps a tv. Yana shigowa suka danna stop sannan suka tarbesa da shewa. Bayan yazauna kowanne acikinsu daga mai cewa yarame sai mai cewa yakara haske. Hmmm shikadai yasan abinda yakeji. Suka zauna hira yabasu labarin duk abinda yafaru dashi yau agidansu zeenat. Suka kama yimasa dariya inji uzyboy kai bakaramin matsoracin mata bane. Rilwan yace naji kyaleni ayanda nake din. Haka suka dauki lokaci suna ta hira daga bisani kowa yatashi yashirya ya tafi harkarsa. Uzyboy akasarin aikinsa da computarsa yake zuwa club yasami 6angare guda yazauna yayi kusan dukkan aikin dayake so. Haka yashirya yatafi netmaye da Rilwan da kuma awwal da sagir. Suka zauna agida yau aranar farko aikin da Rilwan yayi take yasamu wasu makudan kudade wadanda kusan tunda yafara wannan harkar baita6a samun kamar na wannan karon ba. Farin ciki mara misaltuwa yake sai yanzu yatabbatar da aikin da matar nan tayi yayi kyau Sosai. Dare yayi Rilwan yashiga dakinsa yana kwance sai tunanin zeenat yafado masa. Shin wai meyasa ita wannan yarinyar take sona ? Kodai tayi hakan domin ta tozartani agaban mahaifiyarta ne? Hmmm ko dayake takan iya yiwuwa sona din take. Amma haka ake soyayya fisabilillahi? Take yaji wayarsa tana ringing yaduba yaga bakon lamba sabida haka sai yakarata agefen kunnensa. Tareda sallama, muryar mace yaji ta amsa bayan sun gaisa sai yake tambayarta da waye nake magana, karka damu zaka san ko ni wacece amma kafin nan ina fatan ka iso gida lafiya? Eh na iso lafiya wacece yakuma jefa mata tambaya akaro na biyu, tadanyi murmushi sannan tace kadamu kasan ko ni wacece kuma nasani kagane da wacce kake magana. Kinga malama idan bazaki fadamin koke wacece ba karki sake kiran wannan lambar. Tasaki murmushi sannan tace karka yawaita yimin magana matukar kaganni akan computer. Yadanyi murmushi sannan yace zeenat kenan a ina kika sami lambata. Ni ai kamar 6arauniya nake akan abinda nakeso. Hmmm amma meyasa kikayimin haka? Zeenat: me kenan? Rilwan: kinasona baki sanar dani ta hanyar data dace ba, zeenat ; kayi hakuri nayi kuskure nima sai daga baya nazo ina nadamar furta hakan. Rilwan: toh bamatsala amma fa ansami akasi daya. Zeenat: ban fahimceka ba wanne irin akasi akasamu ? Rilwan: bana soyayya. Zeenat : tayaya za'ayi in tabbatar da hakan bayan kuma kusan kodayaushe kana nunamin shauki . Rilwan: idan ke mai tunani ne ai yakamata kigane kiyi hakuri zancen gaskiya ni bantashi aure ba sabida haka babu amfanin nafada cikin rijiyar soyayya domin kuwa fitowa daga cikinta zai zamemin wahala. Zeenat: smile nasan zaka fadi hakan sabida naga alamu atattare dakai amma kasani dai akwai alkawarin dakayimin alokacin dakace karna sake rike ma hannu kace nabari saikagama azumi idan yaso ko guntule hannunka idan nagadama nayi shin ka tuna da wannan? Rilwan: kwarai kuwa natuna amma kuma toh ina zakiganni ayanzu har kisamu kiyi wannan? Zeenat: a ina kasami 'yan matan da naga hotunanku tare acikin computer dinka? Rilwan yakyalkyale da dariya sannan yace kedai 'yan matannan sun tsole miki ido toh wadannan 'yan matan da kika gani kannena ne da 'yan uwana toh ma ina ruwanki dasu koma me atsakaninsu. Zeenat: babu ruwana dasu sai dai sunshiga gonata kuma ba kowaye zai killace gonarsa ashiga yakyale ba kaima kasani. Rilwan yace kinga zeenat inaso nabaki hakuri sabida ni mutum ne wanda yake zaune cikin hatsari karki sake ki shagaltu da sona gara kiyi saurin takama zuciyarki birki daga gangarawa akan hanyar zuciyata domin kuwa hakan zai iya haifar miki da halaka ko kuma kifada cikin nadama wanda har karshen rayuwarki bazaki mance ba. Zeenat tayi ajiyar zuci sannan tace dakata tukunna shin kai din ne zaka jefani cikin halaka da nadama wanda zai dameni har karshen rayuwata ko waye ? Rilwan yace ba haka nake nufi ba da sannu zaki gane cewa kasancewarki tare dani akwai matsala. Tafara magana yayinda idanunta suka cika da kwalla Rilwan atakaice dai baka sona ko? Yadanyi shiru na 'yan dakikai sannan yace bahaka nake nufi ba zeenat nikaina inasonki amma, dakata abinda nakesonji kenan kuma bana bukatar sauran zantukanka idan har kana sona koya kake zan jure kuma zamuyi soyayya dakai, kacire tunanin cewa ayanzu kai bazakayi aureba sabida haka bazaka fara soyayya ba. Domin yin hakan bakomai bane sai haddasa azaba azukatan masoyanka. Aduk lokacin dakatashi aure ni ashirye nake daga yanzu har shekaru goma masu zuwa matukar zakayimin alkawarin amincewa dani amatsayin wacce kakeso. Rilwan yakuma yin shiru sannan yace toh naji amma fa akwai sharadi kafin nan mufara soyayya dake. Tace toh wanne irin sharadi bana tunanin akwai sharadin da zan kasa cikawa matukar zan kasance taredakai amma duk da haka ina sauraronka. Rilwan yadanyi dariya sannan yace sharadin dai shine . novels / HAKAN TAKE part 29 HAKAN TAKE part 29 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 18:52 sharadi na farko duk abinda kikaga nayi wanda bai shafeki ba karkisamin baki. Sharadi na biyu idan na umarceki da yin abu toh koma menene dole zaki aikata. Banaso kiyimin kishiya yawajaba kirabu saurayin da yakiraki awaya awancan lokacin matukar kina sona ba mashi kadai ba duk wani wanda kuke soyayya dashi. Tadanyi shiru sannan tace inbanda kai da abinka yaza'ayi ace masoyinka nagaskiya baicika wadannan sharuda ba koda ace baka gindaya masa suba? Matukar inasonka tilas ne nagujewa dukkan 6acin ranka, matukar inasonka dukkannin abinda ka umarceni dashi tilas ne nayishi matukar baikauce hanya ba. Sannan kuma babu yanda za'ayi macen data kesonka tsakani da Allah tayimaka shariki da wani namijin nadaban, Rilwan duka wannan ba matsala bace abinda nakeso dakai kacire kokwanto acikin zuciyarka, sannan kabani dama na lasa maka zumar soyayya irin tawa natabbata bazaka ta6ayin da nasanin kasancewa tare dani ba, Rilwan yadanyi shiru jiyayi wani irin iska mai sanyi yana ratsa dukkan sassan jikinsa adaidai lokacinda tafara finciko wasu kalamai masu tsuma zuciya. Ina godiya sosai amma sai dai bazan samu zuwa gidanku ba nasan kekuma bazaki gane inda nake ba. Wayace maka bansani ba? Kana zaune ne agida mai lamba... Koda yake ma bazan fadi ba gobe zaka ganni nazo kawai. Yadan saki murmushi ai duk maitanki bazaki gane ba idan kinsani toh kifada mana. Kaidai zaka gani nafiso nabaka mamaki. Toh badamuwa zanga yanda zaki gane gidan nan ai Tace ba matsala. Rilwan yace toh sai da safe ko? Tace yawwa masoyina ina maka fatan kayi mafarki mai dadi taredani acikin soyayyarmu. Nagode nima ina miki wannan fatan. Madallah Rilwan yakashe wayar cikin zumudi wowww ashe haka dadin soyayya yake? Kaduba kagani idan tayi wani kalma daya harcikin kwakwalwar kaina jinake tamkar in nitse yatashi da tsalle daga kwanciyar dayake. Jiyayi an kyalkyale da dariya acikin dakin batareda yaji shigowar mutum ba yajuya yakalli netmaye bisa dukkan alamu yana cikin maye. Rilwan yadubesa yakai bross meyafaru ne naganka ajangale? Yadan tsaya yana tangadi tareda karkarwa tamkar wanda ruwan sama yayiwa dan karen duka dakyar yake magana Kai gara wato kafara soyayya kaima koo? Rilwan yace kaga dan Allah kayi hakuri kaje ka kwanta sai kadawo hayyacinka zamuyi magana dakai. Yadubi Rilwan kai zan 6alla ma wani 6angare ajikin kafa ni zaaka koraa? Rilwan yayi dariya sannan yace masa toh yi hakuri abokina zo muzauna shiyasa nakejin dadin zama dakai ai. Yadan tsaya yana tangadi Sannan yace kai matsa daga nan waye abokin naka? Rilwan yace gaka nan, hmmm kai wallahi baka isa nayii abota dakaiba bari ma kagani ni tafiya ta ma zanyi natafi tunda kai juninka rainin wayo ne,Yanata maimaitawa cikin muryarsa tamkar wanda aka shakesa. Rilwan yana cewa katsaya mana, yace bazan tsayaba dasauri yabude kofa cikin tangadi yawuce dakinsa. Rilwan ya kama yimasa dariya sannan yazauna ya dauki computer dinsa yahau net yadanyi wasu abubuwa sanann yakuma sauka. Washe gari dasafe bayan sunyi karin kumallo suka zauna Rilwan yace musu yanzu a ina muka kwana azancenmu nazuwa adamawa? Sagir yace kaimuke jira kasa mana rana. awwal yace hmm nifa tunani nake dukdacewa nayadda nahakura amma zancigaba da 6oye son Aisha har Allah yabani wacce zata maye gurbinta cikin zuciyata, Rilwan yadanyi murmushi sannan yace yawwa wato harka tunamin hirata da wata budurwa jiya da dare. Sagir yace kaga kaikuma kafara ai. Dazaran ana zance sai kakawo mana batun 'yan matan facebook, dalla can gara ana maka maganan azahiri kana wani zance. Sagir yagyada kai Ni kake cewa gara ko? awwal yace dan Allah karku tada mana hayaniya ni abinda nake muku zance daban kunbi kun hau musu. Sai Rilwan yace toh abinda yadace muyi yanzu ajiye ranar da zamuje. Suna cikin zancen uzairu yashigo hannunsa Rike da computer yace yau bansan meyasa ba network yana rikici ina dab kwasan Naira dubu nari takwas. Rilwan yace toh kayi amfani da wifi mana. Uzyboy yace bari kawai kaikam sai anjima zanyi yanzu akwai bukatar naje offline na kulle komai. Rilwan yace uzyboy gaskiya kana basu wuta fa? No bad kaikam tukunna ma. Weldone. Awwall yadubi uzairu jimana uziboy muna cikin tadi ka katse mana zance. Uziboy yace ok i am sorry you can continue, Rilwan yace muna zance akan tafiyarmu ne, munaso muleka Adamawa acikin wannan makon. Uzairu yace dakyau amma ina fatan bazaku dade ba? Rilwan yace bazamu wuce 1 week ba zamu dawo uzairu yadanyi shiru yana nazari 1 week sannan yace akwai wani target din dana hada ne ina tunanin dole sai anhada karfi da karfe kafin asamu nasara shiyasa bazanso tafiyarku kwanakin nan ba. Rilwan yace haba karka damu idan wannan ne. kaida kakeda netmaye. Netmaye aikin zaiyi masa yawa kyanta ace dukanku kuna nan uzairu yamaida masa zance. Hmmm toh mudai kasan babu yanda za'ayi mufasa tafiyarmu ko? Sagir yakatse masa zancen. Uziboy yace no problom you are free to go sai dai idan ta kwa6e dole kuzo. Rilwan yace toh hakan yayi yanzu inaga sai mubari zuwa rana ita yau sai muje ko ya? Uzairu yace why not kutafi gobe sabida ku dawo da wuri. Rilwan yace kai gobe yayi kusa sosai yakamata na dan huta kaga kwana 14 fa nake azumi nafiso nadan mulmule kafin nan mutafi. Awwal yace yau litinin yanzu dai abinda za'ayi mubari ranar asabar sai mutafi. Uzairu yace ina laifi kutafi ranar alhamis? Sagir yace karka damu uziboy kayi hakuri idan yaso zamuje ko ranar jumma'a idan yaso sai mudawo wata jumma'ar. Yadanyi shiru sannan yace toh ba matsala, suka cigaba da hira. Sai sukaji ana kwankwasa kofa. Awwal yatashi yaje yabude sukayi idan 2 da ita malama barka dai kece kike kwankwasa kofa tadubesa tareda murmushi eh nice, dan Allah Rilwan yana nan ne? Awwal yadanyi shiru yana kallonta daga sama har kasa. Sanye take cikin wasu kaya kanana pink ta daure kanta da dankwali ja da wani dan karamin jaka mai kalar darkred. Takalmar dake kafarta sundanyi tudu wanda hakan yadada kara mata tsawo atakaice dressing dinta yafitarda kyan tsarin halittar da Allah yayimata, fuskarta dagani kasan anyi shafe shafe wani abu kamar fenti asaman idanunta eyeshadow lebban bakinta jazur, Awwal yadauki 'yan dakikai yana karemata kallo sannan yace ke kuma wacece dakike neman Rilwan? Tace malam tambayarka nayi baka bani amsaba kana sake yimin wata tambayar kuma ai yakamata ka barni nashiga cikima nazauna kafin kayimin wasu tambayoyin, Allah sarki ke bakisan Rilwan yatsani 'yan mata irinki ba? Yana da kyau kifadamin ke ko wacece naje nasanar masa kafin nan karki shiga yakasance abin baiyimiki dadi ba, haba malam wace irin zance kakeyimin ne haka tadan ja baya. Sai yace toh ki kirashi awaya mana, tace ok taciro wayarta tana faman kira, sai uziboy yace yadai katsaya abakin kofar ne waye ke sallama, Awwal yawaigo sannan yace wata budurwa ce wai tazo wajen Rilwan, Uzairu yace toh kyaleta tashigo mana, Awwal yadubeta sannan yace kyale kiransa din shigo kawai yabude mata kofa, sannan tashigo Awwal yana biye da ita, tsarki yatabbata ga ubangiji mahaliccin wannan halittar ashe wannan yarinyar tana da kyau haka? Rilwan ya furta zancen zuci baisan da cewa harshensa ta riga ta amshi furucin ba, jiyayi Sagir yace kai Rilwan wacece wannan? Itace mukayi hira da ita jiya awaya, tana dariya takariso inda suke Takalli Uziboy tace sannunku abokansa ya amsa da cewa toh 'yar madam yau kece agidan . Tace eh Ta kariso tazauna akusa da Rilwan har wannan lokacin bai iya furta mata komai ba, tace yadai kana mamakin ganina agidan ku ko? Ya gyada kai alamar eh sannan yace jirani ina zuwa bari na marabceki da wani abu. Yaje yadauko mata drinks tace gaskiya naji dadin zuwa gidan nan amma bazan jima ba zan koma. Uziboy yace komeyasa tace sabida tsaro. Hmmm Rilwan yace amma kafin nace miki komai inaso kifadamin yanda akayi kika gane gidan nan? Tace bakomai kawai ni din 'yar baiwace, Sagir yace kai gara kuce mubaku waje ai kafin nan ku baje mana kolin. Tadubesa sannan tace gaskiya da zaifi kam. awwal yace toh Allah dai yasa agama lafiya yatashi yanufi daki Rilwan yabuga masa harara, uziboy yace nifa babu inda zanje, tace toh ba damuwa kaikam ai babban abokine tunda naganka da computer. Kamarsa kasan menene wallahi ina bala'in son saurayin dayake yawan amfani da computer, Rilwan yace komeyasa? Tace nikadai nasan dalilin saurayina da muka rabu shima haka yake da son computer harma yakoyamin wasu abubuwan, Rilwan yace me dame yakoyamiki? Tace kawai just how to operate the computer yakoyamin bakomai ba. Yayi kyau toh ni zan koyamiki abubuwa dayawa sannan kuma zakiyi amfani kema wajen kara bunkasa mana harka, tace wane harka kenan? Yace karki damu zaki sani. Haka suka wuni suna hira zuwa bayan azahar Rilwan yadauketa yamaidata gida bayan sunje yasanar mata zaiyi tafiya ranar juma'a, tace dan Allah karyamanta idan yatashi yabiyo ta wajenta suyi bankwana kafin nan yatafi. Toh bamatsala ina ga kawai Hakan take. novels / HAKAN TAKE part 30 HAKAN TAKE part 30 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 18:54 Aranar alhamis washe gari zasu tafi Adamawa da dare misalin karfe 7:30 na yamma Rilwan yaje gidansu zeenat kai tsaye yashiga wajen mamarta ta marabcesa sosai sannan takawo masa abinci yazauna yafara cin abincin suka fara tadi sannan tace masa ina fatan kaga chanji acikin al'amuran ka? Yace kwarai kuwa mama nasamu chanji sosai, toh haka ake fata tabashi amsa. Ina zeenat take tunda nazo banganta ba. Tadanyi murmushi sannan tace, tana cikin falo tana kallo. Yace toh bari nagama cin abinci sai muyi magana da ita. Tadanyi murmushi sannan tace toh Allah dai yataimaka tacemin kunsasanta tsakaninku. Yadan dubeta cikin sakin fuska yace mata eh mama dama babu wani gaba ko fada damukayi da ita kawai rannan sabida nakalli Hajiya fadila shiyasa na yadda da abinda tafada akaina dukda cewa zancenta din ba daidai bane. Tadanyi murmushi sannan tace kodai kunya ya hanaka magana? Rilwan yasaukar da kansa kasa tareda murmushi. Ta katse tunaninta sannan tace yawwa dama akwai zancen da zan fadamaka kaga dai zeenat itace 'yar da Allah yabani arayuwa ta gabadaya. Fatana tasamu miji nagari mutumin kirki dukdacewa ayanzu kai yaro ne amma kana iya yin aure idan da hali idan kuma babu hali kana iya kyalewa zuwa wani lokaci mai zuwa. Rilwan ya gyada kai alamar eh. Tacigaba dacewa nasani adan zaman dakayi na kwanaki 14 da zeenat kafahimci yanda take amma inada tabbacin baka karanci halayyanta gabadaya ba amma dan Allah inaso kasota tsakaninka da Allah sannan kazamo mai kula da dukkan al'amarinta. Rilwan yadubeta sannan yace mama karkidamu idan har wannan ne ni nayi miki alkawari zeenat bazata sami matsala ta wajena ba, kuma aduk inda nakalli zata shiga damuwa tabbas bazan kyaleba sai inda karfina yakare. Nagode sosai Rilwan Allah yayi maka albarka Rilwan yace ameeen. Ganinta sukayi atsaye yayinda tazo cikin zumudi shine za'azo ziyara ko awaya baza'a kira asanar damu ba? Rilwan yadaga kai yakalleta tareda murmushi batareda yace komai ba yasaukar da kansa. Ke kam bakya yiwa mutane sallama ne? Mamarta tajuya takalleta alamun haushinta yakamata. Tadanyi murmushi sannan tace yi hakuri mama wallahi na manta ne. Tace toh yakawo miki ziyara ne nizantafi nabaku fili. Tatashi zata tafi sannan yace mama akwai maganar da zanfada miki kuma inaga baikamata ace kintafi batareda nafada miki wannan maganar ba. Tajuyo sannan tace ina sauraronka, yace dama inaso zanyi tafiya ne gobe zuwa Adamawa idan naje zankai sati 1 ko fiye. Tace toh badamuwa Allah ya kiyaye hanya. Suka amsa ameeen. Ta tashi tabar musu wajen. Zeenat tataso tazauna akan taburman dayake kai yadubeta batareda yace uffan ba yakurama fuskarta kallo. Haba dear yakake kallona kamar bakuwar. Yadanyi ajiyar zuci sannan yace zeenat kenan naga kinkara yinkyau ne sosai shiyasa , tadan saki murmushi sannan tace kaima ai hakane? Sannan yace murmushinki yana kara miki kyau sosai. Ta kuma kara murmusawa sannan tace kaikuma ka fara kenan. Yanzu tafiyar ka dinnan babu yanda za'ayi kadagata? Rilwan yace what? Ai sam tafiyata bazata dagu ba. Tace saboda me kace haka? Yace sabida zanje nakalli 'yan uwana daga can zan sanar musu cewa nasami matar aure agarin jalingo. Hmmm tadan saki dariya wace mata kasamu kenan? Yadubeta wata budurwace bazaki santa ba. Tadan saki murmushi. Yakamanninta suke? Yadan gyara zama sannan yace ita farace doguwa kyakkyawa ba mai muni ba. Mai dogon gashi ko ta rufe bazai 6oye ba. Tace kai wannan maganar ka din ai wakace ta wani mawaki dayake siffanta masoyiyarsa. Rilwan yadanyi dariya sannan yace ni dinma ai Hakan take. Suka nitse da dariya, haka Sukayita hira har misalin karfe 10:30pm Rilwan yatashi sannan yace zai tafi zeenat tace haba masoyina bangaji da kallon ka ba kuma zaka tafi. Yace dare yafarayi shiyasa. Tace toh me zai hana ka kwana anan? Rilwan yadubeta cikin raha a ina kenan zan kwana? Tace adakin da kayi kwanaki 14 anan zaka kwana. Yace ke nifa yanzu tsoron wannan dakin nake? Tace toh ba sai natayaka kwana ba? Yace hmmm saboda me.. kinga nifa sauri nakeyi inaga saidasafe. Tace toh badamuwa tunda kaki amma inaso nasanar maka wani zance danaso na tambaya mamata amma nayi tunanin zata hanani hakan,? Rilwan yakalleta sannan yace fadi zancen ina sauraronki? Tace dama naso nayi maka rakiya ne zuwa garinku. Rilwan yadanyi dariya sannan yace zeenat kenan lalle kinasona sosai. Amma kiyi hakuri idan naje zan bawa 'yan uwana labarinki nangaba insha Allahu zamuje taredake ko ina. Karki manta nine wanda kike fatan yakasance tareda ke har tsawon karshen rayuwarki. Tadanyi shiru sannan tace bakomai Allah yakiyaye hanya idan anje kar amanta tsaraba ta. Yadanyi murmushi sannan yace haba toh ko kefa? Amma tafiya ai bataki bace. Washe gari dasafe suka shirya sukayi bankwana dasu Uziboy sannan suka shiga motarsu suka kama hanya. Ana kiran sallar azahar suka iso kai tsaye gidan lauwali maishago sukaje sukayi parking abakin kofa. Ko fito da kayakinsu basuyi ba shiga gidan sukayi tareda sallama. Matarsa ta amsa kamar amafarki takallesu, manyan baki tafada cikin murna takarisa inda suke ta tarbesu Rilwan yamika mata ledar dake hannunsa. Bilal da Fatima suka fito da gudu suka rungumesu. Suna jindadi Sagir yadubi Bilal my boy ya makaranta yace muna zuwa kullum yanzu ma bamu dade da dawowa ba. Sagir Yace yawwa dafatan kuna kokari ko? Bilal yace eh munayi. sagir: lamba nawa kaci asakamakon jarabawarka data wuce? Bilal yace lamba 3 naci sagir yayi dariya sannan yace fatima fa? Bilal yace lamba 2 taci, toh sai ka kara kokari wani term idan yazo sai kazo lamba na 1 kaji idan kazo zan saya maka keke kaji? Yace toh yana jindadi. Suka wuce matan lauwali takawo musu abinci sunaci tazo tazauna kusa dasu. Awwal yace yafama da yara? Tace toh Alhamdulillahi. Sagir yace sai dai hakuri fa mun barku da sungullar yara. Tace Allah sarki ai bakomai yaro nakowane musamman ma maraya. Rilwan yace Allah yasaka muku da alheri. Tace Ameeen. Rilwan yace malam lauwali yana shago ko? Tace eh Rilwan yace zamuje musameshi acan ai. Tace toh amma kyanta kuhuta yanzu zuwa anjima shi da kansa ma zai dawo cin abincinsa. Rilwan yace badamuwa kekam zamuje amma ina labarin Aisha shin tana zuwa nan wajen kuwa? Matar lauwali ta amsa kwarai kuwa jiyama saida tazo ita da kawarta khairat. Ehen hakan yana da kyau. Suka danyi hira zuwa wani lokaci sannan suka tashi suka nufi shagon lauwali. Yana cikin kasuwancinsa suka samesa. Tabbas shagon lauwali takara bunkasa kota ina fuskar jama'a ce kasantuwar shagon tana kallon gidansu nada wato gidan marayu alokacin da suka iso wajen suka kare ma gidan kallo angyara gidan harma antada wasu upstaires hawa daya. Anyi mata fenti pink and red. Gidan yayi matukar kyau asaman gidan and daura wani sign board wanda akayi rubutu manyada manyan Harufa MODERN TECH NIGERIA sunan kafanin kenan. Kadubi yanda aka maida gidan nan Awwal yafada Rilwan yadubesa yace kace dai sun gyara mana gida abin yayi kyau idan zaka fada kace gidanmu, domin ko badade ko bajima sai mun kar6i wannan gidan wallahi ko bamu ba sai an bawa wasu marayun. Sagir yadubesa yace kai kana maganan zancen da bazaiyiwu ba. Rilwan yadanyi dariya sannan yace idan natashi shirya shiri na kawai kubani hadin kai zakusha mamaki yanda zamu kwace gidan nan awajen mai gari. Toh idan lokacin yayi kasanar damu zamu baka hadinkai. Toh Hakan take suka sami waje sukayi parking sannan suka fito. Bisa ga mamakinsu kafin su iso shagon sukaga yafito cikin zumudi yana ambaton sunakinsu daya bayan daya ashe tun motarsu tana nesa yake kallonta harta kariso wajensa ganin sune suka fito daga motar yasashizuwa duk da cewa akwai cunkoson jama'a da sukazo sayan kaya ashagonsa amma dayake yana da yaron gida shiyasa yasami daman fitowa wajensu din. Kune da wannan motar ? suka amsa eh yatambayesu yaushe suka iso ko labarin zuwansu babu. Rilwan yace so muke muyi muku zuwan bazata munshigo ana sallar azahar munje gidanka bakanan matarka tabamu abinci gaskiya muna godiya Allah yasaka. Yace bakomai karku damu hakki ne dake kanmu muke saukewa wannan ba yinmu bane. Suka sami waje shima suka kwashi hira sosai har yatambayi sana'arsu suka sanar dashi cewa aikin computer sukeyi har suka sami kudin sayar mota. Yayi murna sosai sannan yace musu yanzu haka shima akwai gidan da yagina babu kowa sabida haka suje su ajiye kayakinsu aciki su zauna kafin sutashi tafiya. Sukayi masa godiya sannan yashiga motarsu sukaje har gidan yanuna musu gidan. Gaskiya ne gidan yayi kyau sosai, Rilwan yakawo wani tunani aransa Allah sarki tabbas arziki yana tareda mai taimakon marayu da sannu ahankali lauwali yana bunkasa. Maganar da sagir yayi tasa Rilwan dawowa daga tunanin dayakeyi. Muna godiya sosai Allah yakara budi. Yace ameeen ni zan koma yabasu makullin gidan sukayi godiya sannan yafita yatafi suka zauna kai gaskiya Allah yasakawa mutumin nan da alheri Awwal yafada suka amsa ameeen. Rilwan yafitar da computer dinsa yabude yadanyi wasu ayyuka. Awwal yakatsesa da cewa dazu kayi wata magana wanda haryanzu ina ta nazari akanta? Rilwan yadubesa wace zance kenan? Awwal yace kace zamu kwace gidan marayu daga hannun mai gari duk daren dadewa . Rilwan yadanyi dariya sannan yace eh amma fa sai mun shirya sosai. Sagir yace wanne irin shiri kenan zamuyi? Rilwan yace abin danake tunani kenan amma yanzu abinda za'ayi dole ne muje mu binciki kamfanin a6oye wanne irin kasuwanci sukeyi ? sannan kuma taya zamu wargaza shirinsu? wannan ma yana daga cikin abubuwan da zamu fara fuskanta kafin nan aje rikicin wajen dawar mana da gidanmu. Yanzu yau zamuje gidansu Khairat ayau bayan munyi sallar isha'i washe gari inaso kuje kubinciko mana bayani akan kamfanin dakuma ayyukan da akeyi acikinta. Awwal yace idan wannan ne toh faE novels / HAKAN TAKE part 31 HAKAN TAKE part 31 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 18:55 Awwal yadanyi ajiyar zuci sannan yace idan wannan ne toh fa kadauka kawai angama sai kuma me next, Rilwan yace da sannu zamu bi komai karka damu. sagir yace dakata wai wane irin fasali ne haka kake zana mana Rilwan ya haka kawai bazaka fadi dalilin zuwan mu bincike ba kawai kace muje mu bincika? Rilwan yadubesa yace karka damu sagir wato dalilin zuwa binciken sabida munaso musan ta ina zamu 6ullowa wadannan al'amuran ne. Akwai shawarar da zamuyi amma sai bayan kungama zamuyi shawarar hanyar dazamu bi. Suka amsa toh badamuwa Allah yataimakemu. Ameen. Bayan sunyi sallar isha'i suka shiga mota basu tsaya ko inaba sai gidan Alhaji haruna sukayi horn mai gadi yazo yabude yaleka yakallesu sannan yace ah manyan baki yau kune agidan namu? Suka amsa sannan suka wuce sukayi parkin motarsu suka nufi parlo kai tsaye sukayi sallama alokacin babu kowa acikin palon har suka karaso wajen kujerun babu wanda yafito. Rilwan yadan daga murya tareda fadin salamu alaikum. Wa alaikassalam aka amsa Sani ne yafito hannunsa rikeda jaridu yana karantawa, ganin sune abin yabashi mamaki. Ah manyan baki sannunku dazuwa, yakaraso wajensu yamikawa kowannensu hannu sannan yace bismillah kusami wajen zama, suka zauna Sani yace zakuzo shine babu labari? Awwal yace eh saboda munaso muyi muku zuwan bazata ne. Sani yadan saki dariya sannan yaciro wayarsa yakira mahaifiyarsa yace mata Su Rilwan sunzo, cikin murna ta taso daga daki tanufi parlon dasuke din sannan yadauki wayarsa yakira lambar Aisha tadauka hello tafada sannan yace kina ina? Tace ina daki nida khairat sai yace yawwa toh ku fito kusameni a falo. Ta amsa toh sannan tadubi Khairat alokacin tana kwance tana karatu Hamma yace muje musameshi afalo. Khairat tadan zumbura baki wai me zai bamu? . Aisha tace nima dai bansani ba. Kawai cemin yayi nafadamiki muje, shikuma yana da yawan matsala wallahi jikinta da nauyi ta tashi dakyar tareda ajiye littafin dake hannunta suka nufi parlon kai tsaye. Kamar amafarki takallesu suna zaune akan kujerun cikin yanayi na walwala bisa dukkan alamu ayanzu suna cikin kwanciyar hankali tafada azuciyarta sannan tayi hanzarin katse tunaninta dacewa Khairat shin idanuna ne suke nunamin su yaya Rilwan kodai dagaske su din ne? Khairat tace nima dai abinda nake ganowa kenan su din ne amma kamar basu ba sun canja. Jitayi kawai taruga aguje yaya tana zuwa tayi tsalle tarike wuyan Awwal kasantuwar shine mutum nafarko dayake kusa da inda tashigo, ya juya yakalleta cikin zumudi tace shine zakuzo ko waya babu? Rilwan yadubeta ke karki 6alla masa wuya mana sakeshi dan Allah? Awwal yadan hararesa sannan tasakeshi khairat takaraso wajen ita fuskarta cike da haiba, sannunku da zuwa manyan baki zakuzo mana zuwan bazata. Sagir yace kowa dai zancen dayake fada mana kenan. Jeki kawo musu abinci mana kinzo kintsaya sai surutu. Sani yakatseta tatashi tareda cewa toh kuma shiru kakeso inyi. Mahaifiyarsu tace toh me abin musu jeki kawo musu. Tace ai umma ko bai fadaba zan kawo tawuce taje takawo musu abincin suka shiga tadi Mahaifiyar khairat tace haryanzu kuna taraba din ne? Eh acan muke haryanzu, Allah sarki kuna wanne irin sana'a ne acan Rilwan yace Hajiya aikin computer mukeyi irin printing ,photocopy da sauransu. Sani yace gaskiya yayi kyau wallahi kunada sana'a mai kima, amma akwai samu sosai sana'ar ko? hajiya takuma jefa musu wata tambayar, kwarai kuwa ai har mota muka saya sabida samu damukeyi yanzu haka muna shirin sayan gida nema Hajiya shiyasa mukazo nan garin sabida anan mukeson zama. Lalle kuwa yayi kyau Sani yadanyi shiru yana nazarin wannan zancen har mota mukeda yanzu haka ma munzo sayan gida ne anan, wani tunani yazo ransa yaushe yaran nan suka tafi wanda har zasu sami kudi dayawa haka? duka duka baikai 2 years sukayi ba sannan kuma wannan aikin baya yiwuwa sai da na'urori masu inganci sannan kuma wadannan na'urorin sunada matukar tsada shin anya kuwa wanda yatafi yana aikin kwadago acikin shekara 1 da watanni zai iya hada wadannan kayakin? May be sunada mai gida wanda yabasu jari amma idan bahaka ba ina tantama cikin zance wadannan yaran. Aisha talura Sani yana tunanin wani abu sai tatashi ahankali taje kusa dashi sannan tayi tafi da hannunta akusa da fuskarshi cikin hanzari yadago kansa yadawo daga tunanin dayakeyi, Hajiya tace meke damunka ne Sani? Yace babu kawai wani case din da aka bani akotu ne na tuna shi yake yawan jefani cikin tunani, Rilwan yace ai sai ahankali ai aikin kotu akwai cakwakiya Sani yace ai cakwakiya ba kadan bama. Alokacin Alhaji haruna yayi sallama yashigo hannunsa rike da jaka, Aisha taje ta tarbesa sannan yakaraso yana cewa yau baki mukayi haka? Lalle kuwa manyan mutane sannunku dazuwa, suka amsa yawwa Alhaji barka da isowa. Yakaraso yazauna akan kujera suka gaisa sannan yace nakalli wata mota awaje takuce ? Suka amsa eh motarmu ce Alhaji yace madallah yayi kyau sannan yawuce dakinsa. Anan suka zauna suka kwashi hira har misalin karfe tara da rabi kafin nan suka tashi sukayi sallama suka ce zasu tafi sai gobe zasu dawo. Sukayi musu rakiya har zuwa wajenda suka ajiye motarsu Aisha takalli motar laa yaya wannan ce motar dakuka saya? Awwal yace eh itace, gaskiya motar tana dakyau Khairat tafada cikin wasa. Suka danyi dariya sannan su Rilwan suka shiga motarsu suka tafi. Ahanyar komawa Rilwan yace kai gaskiya fa mutanen nan mun basu mamaki musamman ma Sani naga tun lokacin da mukayi maganar munsayi mota harma so muke musayi gida gabadaya yanayinsa ta sauya dukdacewa bainuna mana afuska ba sai yafake da wani case din dayakeyi akotu. Sagir yace no wonder ko shiyasa naga ya zautu cikin tunani saida Aisha tayi masa magana kafin nan yadawo. Awwal yace kwarai kuwa nima na lura da hakan amma ai wannan ba matsala bace tunda mun fada musu sana'armu. Rilwan yadanyi dariya sannan yace eh koma akwai matsala ya zasuyi damu? Kwarai kuwa babu yanda zasuyi damu. Sukayi dariya sannan Rilwan yace nikam ina nema club agarin nan? sagir yace haba kai kuma sai kace wani maye yaushe mukazo har zakayi mana batun club. Awwal yace babu inda zamuje sai gida, Rilwan yadanyi dariya sannan yace toh ba matsala suka je gida. Bayan sun zauna saiga kiran uzairu yashigo wayar Rilwan yadauka cikin hanzari yakara akunnensa tareda cewa hello mugu ya akayi ne? Yace normal kaikuma shikenan kun iso shine ko kiranmu bazakuyi kuce mana kun iso ba? Kabari kawai uziboy yanzu nake shirin kiranku domin tunda muka iso sai yanzu muka zauna, toh ya mutanen ku din suke? Lafiya lau Rilwan ya amsa, uziboy yace dakyau ina sauran garorin nan? Rilwan yace suwaye garorin? Uziboy: 'yan uwanka mana? Rilwan: 'yan uwan nawa kake kira garori? Uziboy : ah toh karya zanyi musu ne? Rilwan : yawwa akwai wata harka anan fa idan ta samu kaima zaka bada gudun mawanka fa? Uziboy: wace harka kuma kenan bayan kasani akwai tawa na 6arota anan yanzu haka ma ina kai , gashi Netmaye banda zuwa club bashida aikinyi yanzu haka ma yana can sai kuma dare yaraba zai dawo adauke, Rilwan: aikaima kana zuwa kuma kana daukewa ni dai ba wannan ba zakaji komai idan natashi yanzu dai zamu iya rage kwanakin da zamuyi mudawo sabida muhada naka aikin idan yaso sai mudawo mugwada nawa, uziboy yadanyi shiru sannan yace ba matsala sai najika. Rilwan yace good sannan yakashe wayar. Washe gari dasafe suka shirya Awwal da Sagir suka Nufi kamfanin shiko Rilwan yafita cikin gari da motarsa yana yawatawa ta ko wane 6angare acikin gari, da yamma misalin karfe 5 na yamma suka dawo gida suka sami Rilwan yana ta faman aiki da computer, suka kariso wajensa sannan yace ya ina fatan kunsami bayanai gameda komai? Sagir yakara matsawa kusa dashi sannan yace kwarai kuwa amma fa tunda mukaje banga wani abu wanda ake producing ba, sai wasu littattafi danake gani suna fita, Awwal yacigaba dacewa da fari ni nazata ma gidan jaridu ne amma sai kuma naga bahaka bane, sagir yace ina tunanin dai wani abu ake shigowa dashi ana kawowa akwai yiwuwar suna kawo wayoyi da wasu na'urori sannan kuma. Dana shiga ciki akwai wasu dakuna dana gani sabbi wadanda ina kyautata zaton ana wani aiki aciki amma banga anbude dakin ba kasantuwar acikin muka wuni. Yadan tashi yatsaya sannan yarufe laptop dinsa yadanyi ajiyar zuci sannan yace dafarko taya akayi kuka sami daman shiga gidan har kuka dade aciki batareda wani yatambayeku ba? Awwal yace kai tsaye mukaje batareda mun nuna musu cewa mu baki bane domin kuwa duk abinda mutum zaiyi idan yaje da full confidence dinsa zaiyi wuya yakasance baiyi nasara ba, sannan kuma kasan kafani dole akwai ma aikata sabida haka ne muka 6atar da kamanni acikin ma aikatar, Rilwan yadanyi murmushi sannan yace kunce kuma bakuga ana aiki ba sai wasu littattafai shin su kuma ma aikatar da kuka 6atar da sawu acikinsu mesukeyi? Awwal afusace yace haba dan Allah me kabi kana tayiwa mutane kididdiga sai kace wani dan jarida kaga ni bazan amsa ba, Rilwan yatuntsire dadariya sannan yaceAKAN TAKE part 32 HAKAN TAKE part 32 Posted by Bashir Sani Fesan on 23 Dec 2016 - 18:57 Rilwan yatuntsire da dariya sannan yace Awwal kenan kai haryanzu sai kace baka fahimci abinda muke shirin yi ba? So muke mu ruguza kamfanin koda kuwa hakan zaiyi sanadiyyar kamamu ne. sagir yace akamamu fa kace? Rilwan yace kwarai kuwa shin kai yanzu kana nufin bazaka iya jure irin wahalhalun daka shasu abaya ba? Gaskiya yakamata kuzamto masu waiwaye domin kuwa idan mu mun wuce wajen natabbata yanzu akwai wadanda suke wajen. Natabbata yanzu haka akwai marayu wadanda suketa yawo lungu lungu suna neman mafaka. Shin kaduba kagani irin yanda muka kasance abaya, wane wahala ne bamu sha ba? Kwanaki nawa mukayi acikin cell? Duka wadannan kun manta shin ko kunsan wannan duk yasamo asali ne tun daga lokacinda maigari yakoremu agidan marayu? Banta6a tunanin cewa kamarku koda ace mutuwa akace kuje kuyi akan hakkin marayu zakuji sanyin jiki wajen aiwatarwa ba. Hmmmm idan bazaku iyaba kawai ku zubamin idanu kugani ko bazan ci nasara ba. Na rantse da zatin ubangiji koda abinda zanyi yasa6a dokar kasa wallahi saina aiwatar idan bazaku iyaba kuzubamin idanu. Sagir yadubesa mekabi kanata wani huruwa kamar kububuwa shin acikinmu akwai wanda yacema bazaiyi bane ko me? Infact kace zaka iya ko kai kadai toh bazamu hanaka ba amma kaje mana kagani ko zakaci nasara. Rilwan yadubesa good gara danaji wannan zancen daga bakinka kawai kuzubamin idanu, yatashi afusace yanufi cikin daki yadauki makullin mota yafita. Suka bisa da kallo Awwal yadubi Sagir amma Rilwan yadauko wani irin rainin hankali kwanakin nan, Sagir yace kyalesa yana ganin shiyake nuna mana wasu abubuwan shiyasa kuma yanaga yadaura mu akan harkarsa mun koya shiyasa yadaukemu kamar wasu yaransa, Ajiyar zuci Awwal yakuma yi sannan yace amma kana ganin idan muka zuba masa idanu bazai je yatsunduma cikin wata matsala ba? Sagir yace karka damu babu wata matsala dazai fada zamu taimakesa amma taimakon da zamuyi masa batareda yasani ba zamuyi. Awwal yace tawace irin hanya kenan? Sagir: ta irin hanyar daya 6ullowa lamarin. Awwal yace toh Allah yakyauta. Rilwan yafita bai tsaya ko inaba sai majalisar wasu matasa masu zaman rashin aikinyi sai karta. Yana zuwa yayi parking na motarsa yafito sannan yakarisa wajensu tareda sallama suka amsa. Yamika musu hannu bayan sungaisa sai yadubi wani matashi sannan yace abokina dan Allah inaso zanyi magana dakai idan badamuwa wannan saurayin yakallesa sannan yatashi sauran samarin suka zurowa Rilwan idanu, Rilwan yadubesa sannunka dai bigguy yace yawwa yakake?. Rilwan ya amsa lafiya sannan yakuma jefa masa wata tambayar. Ya sunanka? matashin ya amsa batareda yasaki fuskarsa ba sunana Mubarak. Malam Mubarak ya jindadi? Yace kaga malam dakata idan kai malam ne toh ni ba malam bane. Kar kasake karenamin hankali danni ba'a rainamin wayo gama ku yaran masu kudi haka kuke idan kunga mutum sai ku daukesa kamar wani danku toh wallahi karka sake karena min hankali nagayamaka. Rilwan yadanyi murmushi sannan yace yi hakuri abokina ni banga abin 6acin rai awannan tambayar danayi maka ba? Kawai yajindadi shikenan? Kai da kake yawo amota nida kaganni ina zaune ina shantakewa ta ai kaine da jindadi bani ba sabida daganinka gidanku akwai naira, Rilwan yace karka ji komai ni mai taimako ne agareka me Sana'arka? Bani da Sana'a gaskiya domin kuwa agarin nan namu idan kace zaka nemi sana'a sai ranka ya6aci ni tunda nagama karatun sekandare iyayena basuda kudin biyamin makaranta kawai nafita nadena daga nan kuma nadawo mai zaman daba, sai lokacin siyasa mukanje mudanyi ehyane mudan sami biyar goma yakarasar maganarsa da dariya kadan, Rilwan yace dakyau mubarak gaskiya ne inason harka da irinku amma abinda nakeso shin amajalisan kun nan akwai wanda yasan inda ake sayar da barasa? Yace kawarai kuwa akwai mai sayarwa ma bari nakira makashi mubarak yawaiga jimana Audu jan wuya ya amsa eh yane Maaga kazo kawai tasamu ana bukatar kayan kari, yace toh matashin yazo da wata jaka ahannunsa Rilwan yadubesa Sannan yace wiwi nakeso Yace na nawa za'a baka? Rilwan yace abani na dubu shida, saurayin yadago kansa yakalli Rilwan sannan bisa dukkan alamu mamaki yacikashi kamar zaiyi magana sai kuma yafasa yayi shiru, mubarak yace abokina sari zakayi ne ko kuma kawai nacakewanka ne? Rilwan yadanyi murmushi sannan yace ni bana cakewa kawai wannan nagayu na ne? Yadanyi dariya sannan yace dakyau gaskiya i deserved to be among your guys, Rilwan yadanyi dariya sannan yace just calm down bross wanann ba matsala bace. Aka bashi wiwi din sannan yaciro kudi Naira dubu goma yace gashi kacire kudin wiwi dinka 6 thousand sauran kuma kadan shana kawai. Gayen yamika masa hannu suka tafa sannan Rilwan yace waye shugaba awannan majalisar? Yace nine nan Uban daba duk garin nan idan kace Audu jan wuya kowa yasanni daga 'yan sanda, masu yakida safarar miyagun kwayoyi kai harma wasu sojojin suna zuwa ina basu kayan cakewa Rilwan yayi dariya sannan yace good yazaro dubu goma sannan yace toh gashi wannan kuma karabawa guys dinka sabida araya majalisa. Audu jan wuya yakuma cewa dakyau gaskiya gayen nan kahadu fa muna godiya sosai. Sannan Rilwan yadubi Mubarak yace kaikuma mubarak zamuje da kai since you want to be included in my guys, sai mun dawo zan baka kasonka kaima ko? Yace bamatsala zamu iya tafiya. Suka shiga mota suka kama hanya. Mubarak yace amma kai bakone agarin nan ko? Rilwan yace a'a ni ai nayi shekaru sama da 18 agarin nan, mubarak : toh ya akayi kuma bansanka ba? Rilwan yace zaiyi wuya kasanni sabida shekaru biyu da watanni nayi ba'a garin nan ba, mubarak: eh gaskiya ne hakan zai iya yiwuwa amma kai dan wayene agarin nan? Tambayar da yayi ma Rilwan kenan saiga wani mai mota yazo yashiga gaban motarsu alokacin da Rilwan yake tafiya cikin speed mai karfi dakyar yayi controlling na motar sannan yaleko yadubi mai motar tareda fadin malam dan Allah kake kula idan kana tafiya da mota domin titinnan bawajen wasa bane, wancan kawai sai ya harbo masa Ashar Rilwan yaleko yakallesa sannan yayi murmushi yacigaba da tafiya, mubarak yace zagin ka fa yayi? Rilwan yace kyalesa, suna cikin tafiya sai yakuma zuwa ya kada kan sterin motarsa yatare gabansu damotar tatsaya Rilwan yataka birki dakarfi motar tayi wani kara sannan yazauna yayi shiru batareda yace komai ba. Su biyu suka fito acikin motar suna daga murya suna tugoma Rilwan ashar yadubi Mubarak suwaye wadannan? Yadanyi dariya sannan yace wannan kamal dan gidan mai gari ne kafita aharkarsa kawai karkayi masa magana. Rilwan yadanyi ajiyar zuci sannan yace dan maigari Kana nufin wannan dan sarkin garin nanne? Kwarai kuwa wannan shine magajin Sarki idan yamutu. Rilwan yace good haka nakeso kai tsaye yafita acikin motar batareda yace uffan ba. Shiko wancan yakaraso wajen da cewa kai dan ubanka me kake cewa ko kasanni waye ne? Wannan titin na garinmu ne kuma zamuyi abinda muka ga dama yakaraso da nufin kama kwalar rigar Rilwan, Kafin ya ankare Rilwan ya daukesa damari saida yaga taurari suna yawo asama, dan ubanka ni ba'a yimin iskanci ko kai dan wayene ni ba ruwana da matsayinka ko matsayin ubanka idan ka kuskura kace zakashiga lamari na wallahi sai na hallaka ka? Wanda ke biye dashi din yazo da gudu zai kama Rilwan da ko kuwa kamal ya daga masa hanny taerdacemai kai dakata kyalesa, hannunsa dafe da kumatunsa yadubi Rilwan kai kamareni? Rilwan yace anmareka tukunna ma wannan ba komai bane sai nan gaba idan katareni da nufin rama wannan marin danayi maka. Yagyada kai sannan yaciro wayarsa kamar zaiyi kira ashe camera yashiga yadagata zai dauki hoton Rilwan yayi tsalle yasa kafa yayi ball da wayar tafadi gefe tayi kaca kaca, Rilwan yace karka fara kuskuren daukana hoto awaya kagane gara kace nabaka hotona ka kaiwa Ubanka nasan idan yaganni zai gane. Rilwan yajuya yashiga motarsa yajata yatafi shikuwa kamal yaje yadauki wayarsa wanda tayi kaca kaca sannan yakoma mota yana huci yadubi abokin tafiyarsa wannan kam dan waye ne? Gaskiya bansani ba abokinsa yabashi amsa, ahmad yadanyi ajiyar zuci sannan yace akwai alamun wannan daya daga cikin 'ya'yan yan siyasan garin nan ne kuma wallahi bari zan fadawa babana abinda yayimin duk ranar damuka sake karawa dashi sunansa sorry wallahi zai san yamarenu. Rilwan suka cigaba da tafiya yadubi Mubarak ya akayi baka fito ba taimakona ba? Yace ai jira nake nagani irin idan sun dan makeka duka daya ko biyu sai in fito in suburbudi 'yan banza sai kuma naga ashe kaima namiji ne? Rilwan yadanyi dariya suka ciga da hira har suka iso gida. Mubarak yariko ledar da aka samusu barasar, suka shiga ciki Sagir da Awwal suna kan computer Rilwan yawuce ko magana baiyi musuba, mubarak yashigo sannan yace sannunku guys Awwal yakallesa sannan ya amsa, daga bisani yawuce daki. Bayan sun shiga daki Rilwan yace dauki wiwi din nan kasha idan kanaso, yace ok Mubarak yaciro yakunna yanasha warin hayaki yafara yawatawa acikin gidan. Sagir da Awwal sukace waye kuma yakesha mana barasa agida, hmm suka tashi kai tsaye suka shiga dakin jimana ya hakane kai kake yin maye agidan nan? Rilwan yadubesu ina ruwanku dashi ? Kunce bazaku iya aikin nan ba shine nikuma nanemo mai tayani, sagir ransa a6ace amma kai Rilwan kama rena mana hankali ma wallahi, kasan Allah duk abinda zai faru saidai yafaru amma wannan sai yakashe wannan hayakin anan, mubarak yace ya isa guys idan akan wannan ne kuke son tada rigima shikenan nahakura yakashe. Sannan yamike akan gado Awwal ya bisa da harara. Sannan suka juya suka fita Rilwan yace good dama abinda nakeso kenan, yawwa wato kasan mene so nake nayi wani aiki dakai, akwai wani Kamfani mai suna Modern tech nigeria shin ko kasan wani abu gameda wannan kamfanin? Mubarak yace kwarai kuwa nasani ai ni nata6a neman aiki acan suka ki daukana wai ban iya amfani da computer ba? yace sai wadanda suka iya aiki da computer kaidai ake dauka ne? Eh haka suke domin kuwa wannan kamafanin tana shigowa da abubuwa dayawa, kasan kamfanin maigari ne hadin gwiwa suke wajen gudanar da ita shida wasu 'yan siyasa wato dan majalisa na jiha da kuma chairman. Amma fa bakowa yasan da hakan ba, mutane sunayima kamfanin ganin na maigari ne amma sam bahaka bane nidai abinda nasani 'yan siyasa suna kawo abubuwa masu muhimmanci awajen, shiyasa ma wajen yakeda tsaro musamman idan kayi la'akari da na'urori da ke wajen, tun kafin kaje akwai wani camera asama wanda yake daukan duk wani abinda ke faruwa tawaje sannan kuma akwai wanda yake kulada abubuwan da camera din ke dauka, Rilwan yayi ajiyar zuci sannan yace tunda kake fafutukan neman aiki awannan kamfanin shin baka ta6a ganin wani kaya da aka buga aciki ba? Mubarak yadanyi shiru yana nazari sannan yace gaskiya babu sai dai takardu nake gani amma bawani abu. Rilwan yace weldone nagode mubarak zamu zauna anan ne kodai zaka koma gida domin iya tambayoyin dazanyi maka kenan? Yace eh toh yanzu dai zanyi gida sabida nasan warhaka angama girki Rilwan yace toh malam Mubarak bari nakaika gidan, yace ok amma nace maka kadena kirana da suna malam fa kawai kakirani da suna maaga domin sunana kenan a area, Rilwan yayi dariya sannan yace nagode maaga dauki barasar da muka saya dinnan gabadaya yace wow gaskiya nagode sosai, suka fita suka kama hanya Rilwan yaje ya ajiyesa har kofar gidansu sannan yadauki Naira dubu goma yabashi yayi godiya sanann yashiga gida Rilwan kuma yakama hanya shine baitsayaba sai gida. Yazo yasamesu sannan yace haryanzu kuna kan bakarku ne kodai zaku hana hannu muyi wannan aikin? Awwal yakece da dariya wayagayaka borno gabas take nasan aikin nan zai baka wahala koda ace zakayi. Sagir yace inace ka nemo wani shayayye ba shi me zai hana bazai tayaka ba? Rilwan yace wato dai har yanzu sai kunyi wasa da hankali na ko? Hmmm toh bari kuji nabaku wani labari yanzu haka nasami masaniya dayawa gameda kamfanin ku gakunan shashashun banza kunje kun yini afilin batareda kun gano komai ba, wace masaniya kasamu?sagir yajefa masa tambaya. Rilwan yace abubuwa dayawa daga ciki akwai mutanenda suka mallaki kamfanin ashe ba maigari ne kadai ba, sannan kuma akwai hannun 'yan siyasa aciki, sannan kuma nasamu bayani akan cewa akwai tsaro sosai musamman na na'ura wato cyber security awajen, wannan shine babbar matsalar dazamu fuskanta sai kuma wani yaro ancemin dan maigari ne munhadu dashi yayi min rashin kunya harma na wankesa da mari. Wadannan sune ababen dana samu daga fitana da yamma zuwa yanzu ni kadai ku kuma kunje kun yini batareda kun kawomana gamsassun zance ba, kutabbata cewa wannan aikin bazai gagareni ba amma da hadin kanku abin zaifi tafiya cikin takaitaccen lokaci balalle bane kuyi amma kuyi tunani shin idan kukayi haka shin kunyimin adalci kenan? Ko kuma kunyi ma kanku adalci kuyi tunani dai? Sagir yayi ajiyar zuci sannan yace zamuyi kuma muna tare dakai amma dolene karika yin shawara damu kafin kayi abu bawai kwatsam kace muje mu aiwatar ba. Rilwan yadanyi shiru sannan yace toh bamatsala idan wannan ne, washe gari dasafe suka shirya sukaje gidan lauwali suka gaisheda shi anan sukayi karin kumallo suka sake dawowa da yamma misalin kar 4 suka je gidan Alhaji haruna ziyara har bayan sallar isha'i suka dawo gidar Rilwan yadauki wayarsa yakira uzairu ya amsa suka fara magana yace yato ina batun mu ya kwana? Rilwan yace karka damu inaga jibi kawai zamu dawo muyi maka aikinka idan mungama shikenan uziboy yace dakyau wallahi naji dadin hakan idan muka hadu duka bazamu wuce 24 hours ba zamu gama, Rilwan yace ashe da sauki ni kuma kasan yanzu abinda na6aro? Wallahi mai tsada ne wata kamfani nakeson ruguzawa, Uzairu yace banfahimcekaba? Rilwan yayi masa bayani daga farko har karshen abinda yake tafiya. Uzairu yace ba matsala idan kunzo zamu tafi gabadayanmu sannan yace dole zamu nemi na'urori, daga bisani muyi creating viruses wadanda zamu aika musu shi awajen tahanyarda zamu sami daman kutsawa cikin dukkan bayanansu daga bisani sai musan ta inda zamu bullowa lamarin. Dakyau haka suka ajiye zance washe gari Rilwan yaje majalisar samarin ya basu kudin karin kumallo sannan yasanar musu zaiyi tafiya kwana 2 zaiyi sannan yadawo, yabi dukkannin majalisar matasa yayi musu alheri sannan yabi duk filin kwallo yaje yasaya musu sabbin ball da jersy, haka yagama dasu sannan kuma ya kama hanyar gidan Alhaji Haruna wani abinda yabashi mamaki baita6a tunanin cewa Awwal na soyayya da khairat ba sai awannan ranar sagir shikuma da zainab kawar Khairat, adaidai lokacin da yashigo yayi arba Khairat tana bawa Awwal juce abaki adaidai lokacin dasuke shakatawa acikin wani rumfa, Rilwan yala6e ahankali kasantuwar basu gansa ba sai ya canja Hanya kasantuwar gidan akwai flowers yana bin bayan flowers yana matsawa zuwa 6angaren da suke ganinsu yayi agabansa suma alamun dai soyewan sukeyi akarkashin wata bishiya wacce flowers ke zagaye da ita, kai la6e la6en me kakeyi? Sagir yajefa masa tambaya yatashi sannan yadaga yatsansa yasa abakinsa yayinda yarufe bakin alamun yayi shiru, ahankali Rilwan yawuce 6angaren da su Awwal suke sai da yaje sannan yadauki karamin dutse yaharbi goran ruwan da suke shana jikin hanzari suka maida hankalinsu zuwa inda akayi harbin atsaye suka ganshi, lalle kuwa wato kowa da budurwarsa nine banda budurwa ko? Awwal yace kaiko kakeda budurwa yakalli Khairat kinga wai mutumin da budurwarsa hargida take zuwa ta dubashi idan taga yayi kwana biyu baije zance ba, tadanyi dariya sannan tace ai soce takawo ga haka, yajuya sannan yakalli Sagir toh kai kuma sarkin kunya yau harda fakewa alungu kenan? Suka kama dariya sannan Rilwan yace ina fatan kun sanar dasu tafiyarmu gobe? Awwal yace eh amma ai kwana biyu zamu dawo? Rilwan yace eh idan munje zanzo da masoyiyata kowa yakalleta. Toh Allah yanuna mana Rilwan yace bari naje mugaisa da hajiya yawuce bayan sungaisa yasanar da ita tafiyar su din sannan yace mata akwai yarinyar daya samu acan yana sonta amma idan yasamu daman zuwa da ita zai kawota sugaisa domin sune zasuje amatsayin iyayensa, Hajiya taji dadin zancen sannan tasanya masa Albarka Rilwan yace idan Alhaji yadawo kisanar masa duk dacewa zamu biyo tanan zan nanata masa. Tace toh madallah. Washe gari dasafe suka bi tagidan lawwali sukayi musu sallama, sannan sukaje gidan Alhaji Haruna nanma sukayi musu sallama Aisha tazo kusa da Rilwan tace yaya ancemin wai zakayi aure kasami mata a taraba ko? Yadanyi murmushi sannan yace mata eh hakane? tace me sunanta? Rilwan yace sunanta zeenat kuma tana sona sosai, yaya kenan toh dan nunamin hotonta mana? Yaciro wayarsa hotontane afuskar wayar yanuna mata tace gaskiya yaya tana dakyau sosai. Rilwan yayi murmushi sannan yace wai ahakanma dan baki kalleta azahirance bane, tace toh yaya yakamata kahadamu awaya. Rilwan yace toh karki damu bari nakirata sai ku gaisa yakirata tadauka hello suka fara magana baitsaya biye mata ba balle tajashi da dogon zance yakatseta dacewa kanwata ce takeson ku gaisa, zeenat tadanyi murmushi sannan tace toh bata wayar mana, Aisha takar6a suka fara magana, auntyna sannunki da warhaka ta amsa suka fara tadi tamkar wadanda suka san juna zancen dai bazai wuce nabaki amanar yayana sai kirikeminshi hannu biyu, zeenat tace insha Allahu Aisha karki ji komai. Suka gama wayar sannan su Rilwan suka kama hanya sune basu tsaya ko ina ba sai taraba. Suka shigo gidan da kayakinsu alokacin netmaye yana fama da aiki a computer ganinsu yasa yarufe computer din yaje yatarbesu cikin marmari suka ajiye kayakinsu Uziboy dawowansa kenan yakallesu yafara murna sannan yace gaskiya kun iso da wuri aranar suka hau aiki suka wargaza net, kafin kace me sunsami nasarar abinda suke nema din, wasu makudan kudade Uziboy yasata daga asusun wani kamfani, very good komai ya kammala yanzu saura aikin wargaza kamfanin Modern Tech wanda shine aiki mafi hatsari dazasu afka ciki, Uzairu yace zamuje dafarko sai mun hada softwire dayawa. Viruses dayawa zamu hada zamu, sunada cctv camera. Dole muma yakamata munema sannan mufahimci yanda ake aiki dashi, Cctv camera yana nufin closed circuit camera, camera ne wireless wanda yakanyi amfani da network din muhalli yana daukan bidiyo dakuma hotunan dukkannin abindake faruwa awajen, kaga kenan idan bamuyi hankali ba cikin kankanin lokaci zasu iya kamamu awannan wajen. Amma akwai softwire da zamuyi amfani da ita angry ip scanner wacce zamu iya hacking din camera din da ita. Bayan mungama da cctv cameras dinsu saikuma computocinsu yana dakyau muyi bincike sosai na'urori nawa sukeda ita awajen suwaye ma aikatan na'urorin sannan kuma wace computer ce mafi amfani awajen? Wannan sune abubuwan dayakamata mu bincika kafin mu tinkari wajen amma zan kara tunani idan akwai abinda zamu saya sai musaya kafin nan mutafi. Rilwan yayi ajiyar zuci Sannan yace ,AKAN TAKE part 33 HAKAN TAKE part 33 Posted by Bashir Sani Fesan on 26 Dec 2016 - 18:58 Rilwan yayi ajiyar zuci sannan yace tabbas akwai aiki agabanmu, Awwal yace kawai kace zamu zamo tamkar aljanu dan gaskiya wannan aikin fa idan mukayi nasara za'a tsoracemu akasar nan, Netmaye yana gefe dariya ta kufce masa yadubi Awwal sannan yace lalle kuwa baka zauna cikin yahoo guys na tsawon lokaci bane . Uzairu yace lalle kuwa zamu zamanto aljanun, washe gari dasafe Rilwan yakira zeenat awaya sannan yasanar daita cewa yadawo zai kawo mara ziyara jindadi take mara misaltuwa shiko yashirya tsaf yanufi gidansu zeenat alokacin da yaje sai yakalli wata mota tayi parking a kofar gidan bisa dukkan alamu mai motar yana jiran wani ne awajen Rilwan yakaraso wajen tareda yin parking agefe yafito yadan gyara tsayuwarsa sannan yakama hanyar shiga gidan yadan waiga domin yaganewa idanunsa mutumin da ke cikin wannan motar. Idanu biyu sukayi dashi azuciyarsa yace Sadauki kuma Meyakawo shi nan? Yadan tsaya yana tunani sannan ya nufi wajen Sadauki tareda sallama yadago kansa yakallesa sannan yaja tsaki Rilwan yadubesa haba oga bai kamata ace akan laifin dana aikata maka wanda yawuce sannan ka yanke alakata dani ba idan kayi la'akari da yanda kake amatsayin maigidana, sadauki yacire glass din dake idanunsa sannan yakallesa yace 6acemin anan, Rilwan yadan tsaya batareda yace komai ba sannan yace kayi hakuri oga ko bazaka yi harka dani ba yakamata ace ka saki jiki dani sannan kuma kayafemin laifin danayi maka. Sadauki yadubesa kai Rilwan wato bakasan ina kisa bako? Oga kisa fa kace? Well nayadda kana kisa amma hakan bazai sa nadena yimaka magana idan nakalleka ba sai dai ka kasheni, sadauki yatashi afusace toh nacemaka banaso, ha'a ka6acemin daga waje, Rilwan ransa ya6aci kawai yajuya yanufi bakin kofar gidan yaja zai bude adaidai lokacin itama ta bude, sukayi idanu biyu dashi jiyayi tayi tsalle ta fada jikinsa you are welcome my dear, yace nagode sosai mushiga daga ciki, tace yawwa naji dadin zuwanka awannan lokacin idan baka manta ba alokacin dakake zaman azumi agidanmu akwai wanda yata6a kirana awaya kaga sunan an rubuta Sadauki. Rilwan yace eh hakane natuna tace toh ai shine wannan mayen kullum cemasa nake yafita aharkata yaki, Rilwan ya waiga yakuma kallon Sadauki mamaki yakamasa dukdacewa akwai tunanin da ta raya masa wancan lokacin zaiyiwu sadauki ne saurayin zeenat dasuke magana, yayi ajiyar zuci sannan yadubeta yanzu wai meyazo yi? Tace wai yazo gani nane. Rilwan yace toh jeki yaganki mana, tace wa ni sam bazaiyiwu ba, fitowa sadauki yayi daga motarsa yakaraso zuwa inda suke tareda fadin Haba zeenat bansan wane irin laifi nayi miki kike azabtar dani da wulakanci ba, ashe dama Rilwan dan Uwanki ne bansani ba? Tadanyi dariya sannan tace Rilwan dan uwana ne kuma masoyina ne, yana sona tsakani da Allah fiye da yanda kake sona sabida haka gaskiya zancen dazan fada maka kayi hakuri kawai iyayena sun aminta dashi kaga kaikuma basu amince dakai ba, sabida haka kayi hakuri kawai adacan nasoka tsakani da Allah kuma ka juya zuciyata yanda kakeso sabida awancan lokacin kai keda ragamarta amma ayanzu saidai incemaka kayi hakuri kawai, Sadauki yatsaya tamkar wani gumgume yakasa yin gaba yakasa baya, hmmm shida 'yan mata keta bibiyarsa datayin soyayyarsu yake banzatar dasu amma wai yau shine zai tsaya yana gani mace tana yimasa irin wadannan kalaman? Rilwan yadan juya yace I m sorry oga bansan cewa budurwarka bace da bazan shiga rayuwarta ba. rufemin baki munafukin banza munafukin wofi Sadauki yafada yayinda zufa ke faman yimasa sharkaf ajikinsa, yadubi zeenat dukkan so da kauna dakika nunamin ashe gabadaya iska ce ko? Dukkan alfahari dakikeyi dani ashe gabadaya zancen baka ne ko? Dukkan zantukan dakike furtamin ashe gabadaya karya ne ko? Kudi na kawai kikaci? Goood hakan yayi kyau kinsamu wanda kikeso amma ina mai tabbatar miki dacewa yau kinsake reshe kinkama ganye, Rilwan yana gefe yayi shiru yana sauraronsa, rike hannunsa tayi kaga my dear zo muje ka kyale wannan, takama hannunsa tabude kofa yana biye da ita yana kallon Sadauki bisa dukkan alamu tausayin Sadauki sun bayyana afuskarsa. Cikin 6acin rai Sadauki yajuya yashiga motarsa yatafi. Shiko Rilwan gabadaya atsarge yake jikinsa amace tadubesa my dear kai kadai nakeso aduk duniyar nan bazan ta6a yimaka kishiya ba kamar yadda ka bukata kafin amincewarka dani amatsayin masoyiyarka, yayi ajiyar zuci sannan yace wannan dakike gani mai gida na ne. Shine mutum nafarko da ya daurani akan harkar danake ciki yanzu, dukdacewa munsami matsala dashi amma harga Allah kalamanun da kikayi amfani dasu wajen korarsa sam batayimin dadi ba. Tadanyi ajiyar zuci sannan tace kayi hakuri my dear dukdacewa maigidan kane shi abaya amma ayanzu zai iya kasancewa abokin hamayyarka. Karka damu da wannan zancen kadauka kawai mun wuce wajen, yadanyi shiru sannan yace wannan mutumin yayimin alheri wanda bazan ta6a mantawa dashi ba, nikuma nayi masa laifi ne wanda bazai ta6a mantawa dashi ba, hmmm dole abin zai dameni, wane laifi kayi masa? Karki damu zaki sani amma tukunna bari naje mugaisa da mahaifiyarki. Ta amsa toh suka je bayan sun gaisa, sannan suka koma gefe ita da Rilwan suka kwashe lokaci mai tsawo suna hira, Rilwan yabata labarinsa gabadaya tun daga farkon rayuwarsa harzuwa wannan lokacin, saida tazubar da kwalla tsabar tausayi bayan yagama bata labari yakula dacewa idanunta gabadaya sunyi jazur dukdacewa shima yana bata labarin bai iya jurewaba sai da kwalla tazubo masa, mahaifiyar zeenat tazo tasamesu alokacin ta lura da idanun zeenat sun rine ta tambayeta meke damunki? Tace idanunta ne yau suke ciwo tace kinsha magani? Zeenat tace a'a tace mata toh maza kije kinemo magani Rilwan kuje karataka , alokacin yasaukar da kansa azaton ta kunyarta yasa yasaukar sai dayadago kansa suka hada idanu ne tafahimci cewa shima idanunsa arine suke shiyasa yake 6oyewa, yace yadai Rilwan kaima idanunka din ciwo sukeyi ne? Ya gyada kai alamar eh, tace sam bazaiyiwu ba Rilwan duk yanda za'ayi akwai abinda ke faruwa tunda kake zuwa banta6a yimaka magana ka bani amsa da gyada kai ba. ke zeenat zo fadamin meke faruwa ne naga launukan idanunku sun sauya kala? Zeenat tayi ajiyar zuci sannan tace mama bazan 6oye miki komai ba amma sai anjima zansanar dake, tayi ajiyar zuci sannan tace menene? Rilwan yace nabata labari na ne? Mahaifiyar zeenat tarike kunkumi tareda tambaya labari kuma shine dakai da ita duka idanunku suka rine? Zeenat tace mama zan sanar dake anjima, tace toh Allah yakyauta sannan tajuya tatafi tabarsu awajen, Rilwan yayi ajiyar zuci sannan yace mata gobe zasu koma Adamawa suyi aikin. Tayi ajiyar zuci sannan tace idan da hali zanyi maka rakiya idan yaso saika gabatar dani amatsayin wacce kakeso. Ajiyar zuci yayi sannan yace awannan karon ma hakuri zakiyi zeenat hakan bazaiyiwu ba. Tace sabida me zakace bazai yiwuba? Yace sabida nasan mahaifiyarki bazata kyaleki ba, sannan kuma .. Dakata idan har mahaifiyata ce wannan ba matsala bace, kawai abinda zakayi ka amince ni nasan yanda zanyi nashawo kanta, Rilwan yayi ajiyar zuci sannan yace toh ba matsala. Nizan koma yatashi tayi masa rakiya har bakin kofa, sannan tadawo tasami mahaifiyarta tabata labarin Rilwan yanda yafada mata sannan kuma zai koma gobe sabida akwai wani aiki dazaiyi idan da hali tanaso tayimasa rakiya. Mahaifiyarta tace akan me zaki bisa? Tadan saki jiki mama fa masoyina ne fa kuma zai gabatar dani ne awajen 'yan uwansa. Tace toh meyasa shi din baisameni yafadamin ba sai ke? Tace mama kinsanshi da kunya kuma nice nafara kawo masa batun harma nace mun ta6ayin batun dake kin amince, tadanyi ajiyar zuci sannan tace toh bazakije ba, haka kawai sam bazaiyiwu ba, tatashi ranta a6ace tawuce daki. Shiko Rilwan bayan yadawo gida yakwanta gabadaya tunani yacika masa zuciya jiyayi wayarsa tana ringing yaduba yakalli Sadauki yadan tsaya yana tunani nawani lokaci har kiran ya yanke baidauka ba, Wani kiran yakuma shigowa yasa hannuns yadauka hello. Yace sai kaga daman daga waya na ko? Rilwan yace oga bahaka bane. sadauki: hakane mana kaima yanzu kataka wani mataki wanda har budurwata zaka kwace hmmm dakyau lalle kuwa ka iya cin amana, amma kafin nan bari na fadamaka wani abu idan har zeenat ce toh fa akwai aiki agabanka, da sannu zaka gane cewa kafada kogin bala'i. Rilwan yayi ajiyar zuci sannan yace oga ni fa haryanzu ina girmama ka kuma bazan dena ba. Amma harga Allah nakosa da irin munanan kalaman dakake furtasu gareni. Gaskiya shawarar dazan baka kawai karike girmanka kar kuma kasake aibata min masoyiya kaji nagaya maka sabida nacanja nima bakamar yanda kasanni da can bane. Rilwan ni kake fadawa wadannan zantukan ? Angayamaka din tunda katsaneni wallahi bazanji kunyar fada maka gaskiya ba, ok bamatsala Sadauki ransa a6ace yakatse kiran sannan yatashi yana cizon yatsa yana tunanin tarkon dazai dana ma Rilwan, washe gari dasafe Suka Shirya kayakinsu duka dama uziboy yaje yasayo musu duk wasu kayakin da ake bukata sannan suka shirya da motoci biyu suka kama hanya. Rilwan da Uzairu suka shiga mota 1 Netmaye, Awwal da sagir. Suka shiga dayar motan suka kama Hanya Rilwan yabi ta gidansu zeenat bisa ga mamakinsa Sai yasamu tagama hada kayakinta tamkar shi take jira, ya kariso wajenta tareda sallama kafin ta amsa ma tace mama ta yarda zan bika muje, yace me kika ce? Tace Eh Rilwan yayi ajiyar zuci sannan yace ina Maman take, tanacikin parlo yakama hanyar parlo zeeenat tabiyosa abaya, yashiga yasameta ta tsintar shikafa, yadurkusa yagaisheta Sannan tace sai tafiyar ne? Yace eh tace toh Allah yakiyaye Hanya dan Allah ka kula da wannan yarinyar amanar dana baka haryanzu tana nan kar ka mance, mamaki yakamasa amma sai yayi shiru yadanyi ajiyar zuci sannan yace karki damu Mama insha Allahu zankula da ita, ta zo ta rungumeta sannan tace ki kula da kanki, tace nagode mama alokacin Hawaye suka kwaranyo a idanunta, tasaketa suka kama hanya da jakar kayanta, suka fito Rilwan yaje yashiga mota uzairu yace wannan fa ina zataje? Rilwan yace zaka gani ai. Yabude mata kofa tashiga baya sannan suka fara tafiya, uzairu yace wai da ita zamu tafi ne kam? Rilwan yace eh, tadanyi murmushi haba malam Uzairu me kabi kadamu. Yace ah babu komai. Alokacin su Awwal sun danyi nisa sabida haka yasa suka iso dawuri, Rilwan yadauki wayarsa yakira Aisha yasanar da ita suna zuwa tare da matar dazai Aura, tayi ta murna tana jin dadi tasanarwa Khairat da hajiya alokacin suka shirya musu kayan taran baki. bayan 30 minutes su Rilwan suka sauka, direct gidan lauwali yaje yayi sallama matarsa tafito suka gaisa sannan yace mata wannan itace surkuwar ku. Suka gaisa cikin fara'a sannan Rilwan yace zai kaita gidan Alhaji haruna su zauna taredasu Aisha tace toh madallah gashi kuma kunzo bangama abinci ba yace bakomai suka tashi suka fito uzairu yana zaune acikin mota suka wuce kai tsaye gidan Alhaji haruna sukayi horn mai gadi yazo yabude sannan suka wuce da jin karar motarsu yasa Aisha fitowa daga ciki domin tasani sune kadai zasu iya zuwa awannan lokacin.. Tafito takalleta cikin murna tazo ta rungumeta sannunku dazuwa Aunty zeenat tace yawwa my sister yakuke. Lafiya lau. Rilwan yace nikuma bazaki tarbeni ba ko? Tace ai kai ba bako na bane itace bakuwa awajena, suka kama dariya Rilwan yadubi Uzairu yace wannan kanwata ce, tadan kallesa tace ina wuni ya dansaki murmushi lafiya ya kuke ta amsa sannan tace muje ciki su Khairat suna jiranmu acan, suka shiga aka tarbesu sosai zeenat taji dadi sosai yanda aka marabcesu agidan Hajiya tace madallah yau Allah yanunamin surukata suna cikin hira saiga Sani yashigo yace ha Rilwan ka kuma dawowa ne. Yace eh wallahi duka mukazo sauran suna masaukinmu nikadaine nakariso nan wajen. Khairat ta tare bakinsa da fadin Hamma kaga budurwar Rilwan yazo da ita sugana. Sani yakariso yana murmushi yamika musu hannu suka gaisa da uzairu yace sannunku bayan sungaisa yace awace Unguwa kike 'yan mata hajiya tace kaji fa Mutumiyar da bata garin nan kake tambayar Unguwarta ai tare suka zo da Rilwan, tare kuma ? akace eh dama tun kafin yakoma yacemin zaizo da ita muganta kafin ayi batun Aure, Sani yace abin yayi kyau sosai gaskiya Allah yatabbatar da alheri suka amsa ameeen. Sannan yace ni zan wuce daki sabida akwai wani aikin danake gudanarwa, yawuce yabarsu afalon. Yashiga daki cike da tantama azuciyarsa, tabbas akwai abin tambaya gameda lamarin wadannan yaran. Wane ubane zai yarje 'yarsa tabiyo wadannan yaran sabida soyayya kawai? Hmmm anya kuwa yaran nan sudena wannan harkar kuwa? Toh wayasani ko iyayenta din ne suka amince da hakan, Tsakanin biyu dai za'ayi daya. Kodai sun gudo nan sabida wani dalili ko kuma ba 'yar gidan mutunci bace, amma dai wannan ba lamarina bane yayi saurin katse tunaninsa, sannan ya kama aiki. Su Rilwan kuma bayan sun zauna na 'yan wasu lokuta sannan suka tashi shida Uzairu sukayi sallama sannan suka koma Hanyar masaukinsu. Uzairu yace amma kai yaron nan baka da mutunci ace kanada santaleliyar kanwa kamar wannan shine baka ta6a sanarmin ba? Rilwan yadanyi dariya sannan yace kaifa gara ne. Yaushe zan zauna ina baka labarin kanwata? Kaga karma kasata aranka sabida wannan gayen dayazo yasamemu mun riga da mun bashi ita, uzairu yadanja tsaki toh da cema nayi ina sonta? Rilwan yace oho dai koma menene. Suka karaso gida sunata cecekuce. Adaki suka samesu suna kwance suka kariso ciki suka samu suna cin abinci a take away. Bayan sun gama ci Rilwan yace yanzu da wanne zamu fara sabida bana bukatar 6acin lokaci. Sonake muyi cracking na abin nan mukoma cikin kankanin lokaci. Netmaye yadanyi murmushi wannan aikin yana bukatar lokaci, yanzu abinda za'ayi zamu daura cameras dinmu asama domin muma mukasance cikin ankarewa, na farko kenan nabiyu zamu install din softwire dinda muka kawo, sannan na 3 kuma kasan harkan nan saida guys kayi dabara sosai bayan mungama guys din zasuyi mana amfani sosai. Rilwan yadanyi ajiyar zuci Aha dafarko dai yanzu ina tunanin acikin dare zamufi samun saukin hacking na cameras din batareda wani ya ankare da abinba kasancewar asakankance sukeda wannan lamarin nasan bazasu ta6a kawo tunaninsu kan abinda muke shiryawa ba. Awwal yace hakane amma fa duk dare bazaka rasa mutum awajen can ba. Uzairu yace karka damu Awwal wasu mutanen kawai zama suke akan computer sabida boge amma bakowaye bane yakeda cikakken nitsuwa tareda maida hankali kan duk wani abinda zai shigo. Yanzu misalin karfe 1 nadare zamu tashi mufara make sure kowa yayi installing duk wasu softwire din nan a computer dinsa ? Sukace toh bamatsala. Dare suka tashi sukayi hacking din cameras din tukunna suka dena daukan duk wasu bayanai dake shigowa cikin na'urorin sai suka fara bincike sosai nan suka fahimci ma'aikatan kamfanin duka basanan sai mai gadi. uzairu yace dole sai waninmu yaje tunda bakowa awajen ayanzu yashiga ciki acikin computocinsu ina tunanin akwai wasu muhimman bayanai wadanda idan muka tura musu virus bazamu iya samun dukkan bayanai damuke bukata ba, Rilwan yatashi yace zan tafi kawai idan naje sai na turamusu wannan softwire dinda mukayi creating dinnan zanje nayi install dinsa acomputer dinsu daga nan duk wasu bayanai dasukayi zamu sami komai anan, eh haka za'ayi amma idan kaje katabbata kasake viruses awajen sannan kuma na'urar dakasaka wannan abin katabbatar dacewa kasaka mata antivirus yanda shi bazata cutu ba. Kaga daga nan zai kasance shi kadaine na'urar da zasuyi amfani dashi mukuma daga nan duk wasu bayanai dasuka shigo zamu samesu tacikin wannan softwire din kagane? Rilwan yace toh bamatsala yadauki computer dinsa sannan yafita karfe 1 na dare da mota bai hadu da kowa ba har ya iso. Wajen yasauka yayi parking din motarsa sannan yazo bakin kofar ya kwankwasa maigadi yatashi yana tambayarsa waye ? Yace nine kamal dan gidan maigari, yatashi ah ranka dade dan Allah kayi hakuri wallahi gajiyace tayimin yawa bacci yadaukeni sosai, Rilwan yayi shiru batareda yakaracewa komai ba gudun kar maigadin yaganosa, kai tsaye yawuce ciki da computer din ahannunsa mai gadin yabisa da kallo kasantuwar yana cikin gigin bacci hakan yasa bai iya tantacewa ba, yaron nan kuma me yakawosa cikin daren nan? Yatambayi kansa sannan yayi shiru badan tsoron cin mutunci ba da na kira Maimartaba batun yaron nan gaskiya yana shiga Hadari sosai cikin daren nan yana dan sarki me zai fito dashi? Yakatse tunaninsa sannan yakoma cikin dalinsa yazauna, Rilwan yawuce kai tsaye kamar yanda suka bincika na'uran dake daki na 5 itace wacce akafi bawa muhimmanci akamfanin sabida hak Rilwan yafara zuwa daki na 1 yashiga yabudeta sannan yatura antivirus din dasuka hada sannan yakuma tura musu softwire dinda zai ke aika musu bayanai gabadaya, daga bisani yadauki ip address nasu sannan yatashi yafita yabude duk na'urorin yatura musu viruses. Sannan yabisu duk yarufe yabar na room 5 kadai abude daga bisa yatashi yadauki computer dinsa yafita, yazo bakin kofa baiga megadi ba yazo yaleka dakinsa yakallesa yana sallar nafila baice komaiba yafita yashiga motarsa sannan ya bankadata yanufi gida... Ahanya yahadu da 'yan sanda suka taresa yakaraso wajensu hankalinsa akwance. Suka tambayesa daga ina yace ma'aikaci ne shi a kamfanin Modern Tech zai koma gidane? Dan sandan yace ina Id card dinka, yazaro Id card din boge yanuna masa dan sandan yakar6a yakalla sannan yamika masa yace masa yatafi. Yawuce kai tsaye ya iso gida alokacin karfe 2:40pm cikin hanzari suka bude suka fara ganin record din dukkan bayanan dake ciki, kudaden jama'a na karamar hukuma idan anturosu maimakon akai banki ko secretariat na local govt sai a bankadasu ta6arauniyar Hanya akaisu kamfanin modern tech bayan sun gama tatsewa sai kuma sauran subiya ma'aikatan karamar hukuma dashi akasari ba'acika musu salary sai anyanke, su Rilwan suka gama satar bayanai gabadaya, sannan Rilwan yace akwai aiki wallahi. Yau nawa ga wata? Sagir yace 25 . Rilwan yayi ajiyar zuci sannan yace bisa dukkan alamu kwanakin nan salary zai shigo sabida haka mukara bincike sosai. Suka koma kan na'urarsu suna satar bayanai nan suka fahimci cewa gobe 26 za'a turo kudi ta wata 6arauniyar hanyar da ake biyowa da kudi wanda ba kowaye yasani ba, very good munyi sara akan ga6a uzairu yafada sannan yace zamuyi musu karaf daya maganin bagidaje amma yanzu atunaninka tayaya zamuyi mu kwace wadannan kudaden dazasu shigo din nan. Netmaye yace gaskiya akwai damuwa amma ina tunanin zaiyi wuya ace jami'an tsaro ne zasu bi 6arauniyar Hanya dakudin, Awwal yace haba abu ne mai sauki muda mukeda Guys agari, Rilwan yace hakane amma kasan dai kosu guys dinma saida makami zasu iya tunkarar motar 6arayi. Uzairu yace ko akwai inda kukasani zamu iya samun bindiga? Rilwan yayi ajiyar zuci sannan yace eh toh gaskiya ...... HAKAN TAKE.. Rilwan Re闂佽偐鍎ゆ慨顡瞴 09035668852, duba da yadda nake samun korafe korafe bisaga rashin kawo labari dawuri, a6angare guda kuma wasu suna kawomin korafinsu akan wasu labarun damukayi abaya kamar SANADIN CHAT da BAKANDAMIYA hanyar dazasubi sukaranta, wato abinda nakeso kuyi la'akari da shi website din danake sawa aciki server dinta sun rufe wato shafin www.Reallywan.m ywapblog.com dama aciki nake sawa yanzu kuma shafin yadena aiki, sabida haka nake hada wani shafi koda karami ne amma zanyishi bisa tsari yanda zan bawa duk wani maziyarci daman yin rejista aciki sannan idan yakaranta posting zai iya comment aciki gaba kadan zan gabatar muku dashi sannan kuma ga ayyuka danke fama dashi wannan yana 1 daga cikin dalilan dasuke hanani samun daman kawo labarin Hakan take dukdacewa labarin yakusan karewa. Amma insha Allahu zamu kara kokari sosai wajen takaita lokacin kawowa. Home / HAKAN TAKE novels / HAKAN TAKE part 34 HAKAN TAKE part 34 Posted by Bashir Sani Fesan on 05 Jan 2017 - 20:34 yace eh toh gaskiya nikam banida wata hanyar samun bindiga, uzairu yace yana da kyau ataresu damakami koda na boge ne. Awwal yace kai akwai matsala fa awannan lamarin idan kuma aka kama mu da makami fa? Netmaye kajika ai ? Wannan harkar tamu matukar kana tunanin cewa za'a kama ka toh wallahi bazaka tsinana komai ba, tunda nashiga wannan harkar jami'in tsaro ko kamshinsu banji ba balle sukamani amatsayin mai laifi. Kagane yanzu abinda zamuyi koma menene kawai mudebi guys din mutafi dasu amma karmu sanar dasu cewa kudi zamu kar6a kawai abinda zamuyi dasu shine mutare motar mu kwace abinda ke hannunsu idan muka dawo mu tsakura musu nakashewa ko ya? Rilwan yayi ajiyar zuci sannan yace toh yanzu dai Allah yakaimu goben. Toh amma musake musu cctv camera dinsu. Dasauran abubuwansu tunda softwire dinmu tana yimana satar bayanai Netmaye yafada. Bayan sungama komai suka rufe na'urorin sannan suka kwanta bacci misalin karfe 8 suka farka sabida gajiyar dasukayi tasasu makara. Bayan suntashi sukayi sallah sannan sukaci abinci uzairu yace Rilwan kaje ku gana da guys dinka sannan katabbatar musu cewa zamuyi wannan aikin acikinsu kaza6i mutane 3 masu karfi sannan kuma yakasance sunada experience, yace ok karkadamu basai naje ba, yaciro wayarsa yakira maaga yadauka suka fara magana, yace hello oga dafatan kadawo , Rilwan yace eh nadawo tun jiya da rana yanzu ina bukatar ganinka cikin gaggawa idan kana da halin zuwa? Yace haba oga aikai na daban ne dole ma inzo yanzu kana ina? Rilwan yace ina gida. Maaga yace toh gani nan zuwa.. Jim kadan yazo yasamesu Rilwan yasanar dashi abinda suke bukata.. Wannan ba matsala bace maaga yafada sannan yace jim kadan zasu zo sutafi. Yatashi yatafi anjima misalin karfe 9:30 na rana sukazo su uku. Maga,Audu janwuya, dawani matashi su uku, da barandami da Adda suka zo, suka sami su Rilwan suka shirya, Rilwan da Uzairu suka zauna agida suna watching dinsu da computer ta hanyar earpiece command sannan Awwal da Sagir dakuma netmaye suka Hadu da sauran guys dincan suka kama Hanya. Earpiece command wani nau'in na'ura ne da ake amfani da ita ta computer wacce akasari sojoji suna amfani daita awajen yaki tayanda wasu jami'an suna gida suna kallon dukkan abinda ke faruwa awajen yakin sannan suna bada umarni wa commandan sojojinsu dake filin daga yayinda commandojin ke sawa akunnensu wannan shine army earpice commmand. Suka kama hanya kai tsaye suka shiga cikin daji daidai wannan hanyar suka fake motarsu acikin jeji ta yanda ma babu wani wanda zaisan cewa akwai mutum awajen. Suna communicating da su Rilwan nanfa suka sanar dasu cewa akwai motar datake zuwa su fito su binciketa. Tasowarsu suka lura da cewa motar tana zuwa ne cikin matsanancin gudu. Kafin su ankare motar harta iso inda suke. Netmaye daya fahimci hakan sai kawai yaja motarsu aguje kasantuwar shine acikin motar. Agabansu yafito , yataka birki atsakiyar hanya. Direba din wancan motarma nan yanuna kwarewarsa wajen iya tuki. wani juya motar ta tashi yayi sama sannan ta fado agefe sai ya yanka cikin daji, Netmaye yadanna baya yabisa yaje yasha gaban motar yakuma juyawa yana neman sauya Hanya sai tayar motarsa na gaba ta gefen dama tafita, motar tayi tambul sannan ta kife akasa, a guje su Awwal suka kariso wajen da makaman dake hannunsu. Suka mirgina motar sannan suka ciro mutanen dake cikin sunji jiki suka saukesu agefe. Netmaye yazo yatsaya yafito yana tafi dakyau dakyau babban direba gaskiya ka kwarance wajen iya tuki. Amma fa kayi hakuri yau ka gamu da ubanka. Su Awwal yazagaya yaje yabude boot din motar yaciro wasu jakunkunan guda 2 acike makit. Ko tsayawa dubawa baiyba.yadaukesu yace yasaka amotarsu sannan sukazo suka taru akansu yatsaya akan direba tacikin earpice command suke magana Rilwan yace Sagir katambayi wannan direban me suka dauko? Sagir yatambayesa yace kudine. Daga ina sannan kuma ina zakukai. Wannan mutumin yayi masacikakken bayani kamar yadda suka gani acikin bayanan dasuka sata ana'urar. Hmmm dakyau wannan daman dukiyarmu ce Sagir yafada sannan yace take care kumaida hankalinku akanmu domin kuwa idan wannan kamfanin taku tayi wasa saimun tada ita daga aikii. Koma dai menene zamu baku sako idan kuka koma saikubawa manager dinku sannan ku kaiwa maigari. Sannan kuma kugayama chairman yaji tsoron Allah yadena bin 6arauniyar Hanya da kudi yana salwantar dasu. Sannan kugaya masa koda account dinsa zai rinka turawa inada tabbacin saimun dandatsa account din muncire abinda muke bukata. Direban yayi ajiyar zuci sannan yace mungode sosai tunda bakashemu zakuyi kuma in Alllah ya yadda zamu isar muku da sako, yawwa Audu jan wuya yazo da barandami sannan yana fadin banayiwa 6arawo sassauci dukdacewa ni dinma ina sata amma satar danakeyi dan nasamu abinda zanci ne. Dan Allah dan Annabi malam kayi hakuri karka kashemu. Direban yafada yayinda yakwanta akasa yana bawa Audu janwuya hakuri. Yadanyi dariya sannan yace da ace akwai sassauci da iyayen gidanku bazasu na cimana zarafi agari ba. Yanzu haka idan kabincika prison akasari yarana ne aciki sabida sun aikata laifin da bai taka kara yakarya ba. Toh yau babu abinda zai hana ni sarema kowanneku hannu wannan shine sako mafi dacewa dazaku tafi dashi.. Rilwan yace ma Netmaye cire earpiece dinka kabawa Audu jan wuya. Netmaye yace dakata Audu yatsaya jikinsa na bari Netmaye yakaraso kusa dashi sannan yacire earpiece command dinsa yamika masa yace saka wannan akunnenka Rilwan yanason magana dakai. Yadanyi ajiyar zuci sannan yakar6a, yasaka akunnensa sannan Rilwan yafara yi masa kirari. Uban maza gagara gasa sun buga sunkasa ka buga sun watse. Barde kake maganin sadaukai. Yadanyi murmushi sannan yace oga wannan kirarin naka haka? Rilwan yace kayi hakuri inaso kakyale wadannan mutanen ahaka, Audu yace kabari kawai na cirema 'yan banza Hannu, Rilwan yace no karka ta6a su yanzu akwai nangaba. Yace ok toh bamatsala. Yatashi yana huci kunci albarkacin oga amma idan bahaka ba da nayi filla filla daku yau dinnan, yatashi sannan Rilwan yace kuyi kokarin kubar wajen cikin hanzari. Toh bamatsala. Suka fada Sannan suka shiga motarsu suka kama Hanya, Rilwan da Uzairu suka tafa sannan sukace Allah yadawo daku lafiya. Rilwan yatashi zai fita juyawan dazaiyi sai yaganta abayansa tana tsaye. Mamaki yacikashi ha'a zeenat meyakawoki wannan gidan kuma? Wayace miki anan gidan muke? Ya akayi kika shigo bamuji shigowarki ba , tadanyi ajiyar zuci sannan tace nasan zakayi mamaki ai lokacin dana shigo Hankalinka yana kan computer, nikuma dama atsarina ba'ayimi magana matukar ina kan computer haka nima banayiwa mutum magana matukar naganshii akan computer, Rilwan yadanyi ajiyar zuci sannan yace ba wannan ba tukun ya akayi kika san wannan gidan? Tace haba my sweat heart sai kace wata 6arauniya dan nayi maka ziyarar bazata? Kayi hakuri nasami zama ai ko baka tambayeni ba zan sanar dakai. Uzairu yakalleta sannan wani zance yazo zuciyarsa anya kuwa wannan yarinyar batada wani nufi akanmu? azuciyarsa yace anyway zamuyi maganinta. Yatashi akan computer dinsa sannan yafita yabasu waje. Rilwan yamaida hankalinsa wajenta sannan yace samu waje kizauna, tazauna sannan tace my sweatheart lafiya kuwa idan bakason ganina ai saika fadamin idan yaso nafita nabarma waje. Rilwan yace no yaza'ayi kuma naki son ganinki? Kinmanta ne you are my best. Tadanyi murmushi sannan tace sai yanzu nadanji sanyi acikin zuciyata , Rilwan yadan saki dariya sannan yace menene silar samun sanyi acikin zuciyarki haka cikin takai taccen lokaci haka? Tace sabida naganka, tunda safe natashi cikin kadaici su Aisha sun tambayeni me ke damuna nasanar dasu rashin ganinka akusa dani ne silar wannan damuwar. Yadan sosa keya sannan yace kedai akwai ki da zolaya, tace bawani zolaya takuma tashi ta matso inda yake, yadan kalli cikin idanunta sai tayi murmushi sannan yace mata yadai? Tace babu kawai ina kare maka kallo ne. Yakuma yin murmushi sannan yace dan Allah karkisa na haukace koma kizauna. Tadanyi ajiyar zuci sannan takoma gefe kan kujerar da Uzairu yatashi tazauna sannan ta fuskanci computer dinsa kasancewar computer din uzairu na gaban kujerarsa, Rilwan yace kinga dan Allah ki kyale computer dinnan nafara jin dadin zance dake. Tace saboda me zakace in kyale? Rilwan ; sabida idan kina kan computer ba'a yimiki magana, tadanyi dariya sannan tace toh wannan dokar na karyata amma iya yau kadai, zamuyi zance kawai kaima kayi aikinka nima zanshiga inda nakeso. Rilwan yayi ajiyar zuci sannan yadawo da hankalinsa kan computer dinsa, yace bakiyimin bayanin yanda akayi kika gane nan gidan ba? Tace Au sorry namanta ne jiya akwai gidan da mukaje gidan wani mutumi malam lauwali. Yace eh tace toh shine naje nasamesa agida sannan yahadani da mai adaidaita yakawo ni nan, Rilwan yayi ajiyar zuci sannan yace amma fa kina yin wani kuskure my sweat, tace kamar me kenan? Yace kinsan mutanenmu na Adamawa akwai kunya sam zasu rika miki kallon bakida kamun kai, sabida haka please you should act the way they act karkisa sufara zargina akanki please, tadanyi shiru tana jinsa duk dacewa akasarin hankalinta yana kan computer din amma sai da tamaida masa zancen dafadin haba my love ai kaima kasan ina iya bakin kokari na. Yace nasani amma kikiyaye dan Allah yanzu ma zanso ki koma gida domin gudun kada su Khairat su nemeki, tace toh zankoma amma saidaifa mutafi tare, Rilwan yace sam bazaiyiwuba akwai abinda yake jira,. Suna cikin zancen saiga Uzairu yashgoi da magana da karfi ke me haka dan Allah sauka min akan na'ura ta waiga takallesa dasauri tasaka hannunta a keyboard ta caccaka wasu madannai sannan ta tashi da alamun ranta ya6aci ta waiga takallesa haba malam Uzairu akan computer ne zakayimin Irin wannan tsawar? Yakariso ransa a6ace baice mata uffan ba yakalli Rilwan yayinda idanunsa suke kallon zeenat din, kaikuma kana kallonta bazaka hanata ba saitayimin 6arna, Rilwan yace haba Uziboy ai my love ta iya computer sosai kawai kaine baka sani ba, tatashi sannan tace my Love gaskiya ni tafiya zanyi nafasa tsayawarma tunda abokinka kori na yayi. Rilwan yace toh bari narakaki koda bakin kofa ne, tace banaso, tafita afusace daga parlon tashigo farfajiyar gidan sai ga su Awwal sunshigo aguje damotarsu, takoma gefe tatsaya a tsorace, Awwal yafito yakalleta sannan yafara zancen zuci gaskiya wannan yarinyar banga amfanin zuwa da ita garin nan ba, abanza tana zubarwa mutane mutunci yayi saurin katse tunaninsa Sagir yace haba zeenat saida kika biyoshi har nan? Tadanyi murmushi sannan tace son danake yimasa harma yafi haka , gashi nan ma nazo yakoreni, Netmaye yafito bisa dukkan alamu ganinta awajen ya6ata masa rai yace toh basai kitafi gida ba, tace basai kafada ba, Audu janwuya yata6a maaga sannan yace wannan wacece, maaga yadan kasa da murya sannan yace nima bansanta ba. Suka fito suka tsaya sannan takama hanya taje ta bude kofa tafita, sai da suka tabbatar tafita sannan suka fitar da jakar suka shiga dasu cikin dakin. Audu janwuya yadubi maga menene acikin jakar nan, maaga yace nima bansani ba, Audu yatashi yace koma menene saina gani, yaje kai tsaye yazige zip din jakar sai yakalli takardu sai kuma yarufe yakara bude dayanma yaga takardu. Awwal yakallesa sannan yayi murmushi haba malam Audu kadena irin haka, yadanyi murmushi sannan yace balaifi bross share kawai suka shiga ciki. Da jakar suka sami su Rilwan suna kace nace da Uzairu, yace zeenat tashiga bangaren dayake ajiye wasu information kuma yana tunanin tagani, Rilwan kuma yace koda tagani babu abinda zatayi zaiyiwu ma tashiga ne luckily bawai danufin neman wani abu ba, Uzairu dai abin baikama hankalinsa ba ganinsu Awwal sun dawo yasa suka tsayar da sa'insar dasukeyi din, sannan suka marabcesu suka kar6i jakar suka kaita wani fanni na gidan. Sannan Rilwan yaje yadauki wasu kudi masu yawa yabawa su Audu jan wuya suka kar6a suna godiya sannan suka fita suka tafi, uzairu yace ina fatan acikin guys dinnan babu wanda yakalli abinda ke cikin wadannan jakar? awwal yace Audu yabude kuma yagani amma bana tunanin yakalli kudi aciki sabida abin ashirye yake kudaden suna can kasa. suka binci sannan sannan Rilwan yace abinda za'ayi wadannan kudaden mukaisu banki. Sukace kwarai kuwa sukaje suka adana abanki makudan kudade. Mutanen kamfanin modern Tech suka jira zuwan kudi amma sam shiru abu baizo ba. Suka kira lambar masu kawo kudi lambarsu baya tafiya. Daga nan suka kira chairman yace yaturo su dakudin. Amma sam basu iso ba. Sabida haka ya turo wasu mutane su duba wannan 6arauniyar Hanyar ko akwai abinda ke faruwa , suka kama hanya isowarsu wajen suka kalli alama dukdacewa babu motar abakin hanya tana cikin jeji amma yanda ciyayin wajen suka tone ne yatabbatar musu wannan motar tashiga jeji. Sabida haka sai suka ajiye motarsu awajen suka fara bincika bangaren wajen. Basuyi wani tafiya mai tsawo ba suka taddasu akwance babu halin tafiya gakuma motarsu taya ta fita, suka kariso wajen suka tambayesu meyafaru ? Wasu matasa ne sukayi mana fashi nayi iya bakin kokari na domin ganin nagudu da wannan kudin amma sai tayar motata tafita. nanfa suka kwashe duk abinda yafaru suka zantar, aka daukesu akasasu cikin mota sannan suka dawo dasu gari akasaukesu a asibiti. Labari ya iso kunnen maigari da chairman. Kafin kace me sunje asibitin suka sami wadancan direban yana kwance agadon asibiti maigari yaje ya wankesa damari yana huci akanme zakayiwa mutane wasa da dukiya. Ka kosan wannan dukiyar dukkan jama'ar dake karamar hukumar nan ne , Kauyuga da lunguna duk wani ma aikaci zaizo kar6an salarinsa. Chairman shiru yayi yakasa magana yana tunanin yanda akasan hanyar dasukebi dakudin. Duk yanda akayi akwai hadin baki acikin wannan lamarin yafada sannan yace babu yanda za'ayi haka tafaru. Tunda duka duka mutane 5 ne suka san hanyar damukebi da wannan kudin, daga ma aikatan kamfanin modern Tech sai kuma ku direbobina. Suna cikin wannan wayar maigari tafara Ringing yadauka yalli lambar manager dinsa ne sannan yakara akunnensa suka fara magana maigari yasanar dashi abinda ke faruwa. Sannan manager yace ranka yadade jiya danka yazo kamfaninmu dadare bayan muntashi kuma yayi mana shige shige ana'urori wanda yabirkita mana kansu, gaskiya ranka yadade kajama wannan yaron naka kunne. Mai gari yace manager wai me kake fada ne? Yace nasami na'urorinmu abude kusan dukansu a sakankance hakan yasa virus suka duru sosai natambaye maigadi wayashigo yayi amfani dasu yacemin jiya kamal dinka yazo nan misalin karfe 1 na dare, mai gari yace karya ne wallahi karya yakeyi sam haka bazata ta6a yiwuwa ba. Jiya muna tareda yaron nan har karfe 11 na dare yashiga dakinsa ina parlo har misalin karfe 3 ina nafila bai tashiba balle yafita sai da safe sabida haka wannan maganar nashi karya ne, manager yayi ajiyar zuci sannan yace toh zamu bincika dai ranka dade. Chairman yadubi mai gari sannan yace lafiya kuwa rankadade dawaye kake waya? Maigari yadubesa banda manager mana da wani zancen banza wai sunje sunsami anyi bincike acikin na'urorin kamfani wai kamalu na ne yaje yayi da dare misalin karfe 1 . Chairman yace bani wayar muyi magana. Maigari yamika masa wayar yaduba saiga yakatse kiran. Sai yamaida masa wayar yaciro tasa yakira lambar manager din. Sannan yace wai meyafaru da na'urorin kamfanin? Manager yace wani ne yashigo har wajen yabudesu kuma ina kyautata zaton yafita da bayanan sirri. Chairman yadanyi ajiyar zuci sannan yace wanene wannan? Rankadade wannan shine abinda yake damuna bamusan waye bane. Nakuma tambayi megadi yacemin kamal dan maigari ne. Chairman yace toh me amfanin security camera dinda kukasa muka saya da makudan kudade kubincika mana kugani waye yashiga alokacin. Manager yace ranka dade wallahi bansan damuwar wannan camera din bama itama naduba daga misalin karfe 1 zuwa biyu da rabi na daren jiya bata dauki bayanan komai ba. Asali ma kamar kasheta akayi. Chairman ransa ya6aci kai malam manager karku raina mana hankali mana, dama camera din bata aiki dadare ne. Yace ranka dade tanayi amma bansan me yasameta ba, chairman yace wallahi kusan yanda zakuyi kushawo kan wannan matsalar ayau. Idan aka sake samun akasi wallahi kowannenku zai dandana kudarsa, manager yace toh ranka dade. Sannan yakatse kiran manager yadubi maigari kaji wani zancen banza fa, yaza'ayi irin wannan abin yafaru haka kurum batareda anshirya abin ba? Wannan zancen banza ne. Maigari yayi shiru kaman bazaiyi magana ba daga bisani yace kyalesu idan sukayi wasa wallah sai sun gwammace fara yin harka damu matukar suka ci amanarmu, shiko manager yana gama magana awayar yatashi abirkice haba jama'a duk yanda za'ayi wannan abin akwai wani dan iskan dayashigo nan. Yakoma yasami megadi, yace baaba megadi kace jiya kamal dan maigari yazo nan. Yace kwarai kuwa. Yadanyi ajiyar zuci sannan yace ba kamal bane yazo Baba 6arawo ne yazo kawai yarena maka hankali ne. 6arawo kuma me yadauka to? Manager yace kawai yasati bayanai ne, mai gadir yace toh bayanai kuma ? Ahbbb ni na zata ma yakwashe duka na'urorin dake ciki ne wannan 6arawon ma wawan 6arawo ne bai iya sata ba. Manager yakallesa haushi yakamashi hmm shiko ya iya sata gashi can ina kyautata zaton satar kudadenmu dazasu shigo din nan ansamu bayanai din dana ajiye ne akashigo tanan yana rike da kunkuminsa yakarisa bayani, maigadi yace kamanya kenan? Manager yayi tsaki sannan yace baba kaikam bazaka gane ba ai. Yajuya yakama hanya yakoma ciki gaskiya dole na tsaurara bincike acikin computer din nan, a6angarensu Rilwan suka shirya sannan suka kai kudi banki sukaje gidan Alhaji haruna suka wuni sai dare suka dawo suka kwanta da dare suka shiga na'urorin suna bincike cikin bayan dasuke samu daga cikin softwire dinsu sai suka sake cin karo da wasu bayanai na kudaden da zasu shigo gobe ta wani barauniyar Hanya. Dakyau Rilwan yafada sannan yace another chance, yanzu gobe yaza'ayi? Yatambayesu. Sagir yace yanda akayi yau mana haka za'ayi wannan ba matsala bace tunda akwai guys. Uzairu yadanyi shiru sannan yakatse tunaninsa da cewa shin kuna tunanin anya kuwa ba tarko suke son hada mana ba? Netmaye yace bana tunanin hakan domin kuwa bakowa bane zai iya kawowa azuciyarsa cewa shirin damukayin nan ta wannan hanyar muka tsara ba, toh bamatsala gobe sai ku shirya amma kuyi taka tsantsan sukace bamatsala. Washe gari da safe suka tashi suka shirya sannan suka nemi su Audu jan wuya da maaga duka kama hanya kamar yadda sukayi jiya awannan karon Awwal ne ke tuka motar sukaje suka la6e suna zaune suna dan tattaunawa dasu Rilwan tacikin earpiece command, sai ko sukaji motsin mota tana zuwa Netmaye yace bross naji motsin mota kuduba mana , su Rilwan suka bincika area din wajen suka hango wata mota karamar starlite daga nesa amma dukkan glass dinta baki sannan kuma tana tafiya da hankali. Uzairu yace kuyi hankali da wannan motar akwai alamun makarkashiya tattare da wannan motar, Rilwan yace wace makarkashiya kuma ku afka musu kawai dazarar sun iso inda kuke. Ba matsala ahankali motar ta iso wajensu saiko suka fito bakin hanya suka ajiye gungumen itace tayanda motar bazata wuce ba, masu motar suka kariso wajen sannan suka fito yadai lafiya malam? Maaga yadamki kwalarsa yace kwanta Audu jan wuya yazo tabayansa yatattaresa sai daya kwanta dayan yafito lafiya kuwa malam? Daka masa tsawa sukayi kwanta yakwanta sannan Netmaye yaje yabincika cikin motar yacikaro da wata makekiyar jaka guda daya yadaukota yafitar sannan yadubi mutumin dake kwancen me acikin nan? Yajefa masa tambaya, bakinsa na karkarwa yace takardu ne. Netmaye yace wane irin takardu? Takardune na kamfanin modern Tech yayi ajiyar zuci sannan yace toh mun kwace kaji sai ku koma kuce musu 6arayi sun tareku sunkwace, yadauki jakar yaje yasakata acikin motarsu sannan yacema direba din tashi kaje kasace iskan tayar motanka. Yace toh yatashi jikinsa na rawa yaje yasace sannan yace mutafi sukaje sunshiga mota sunyi mata key sai sukaji wannan mutumin dake kwance yadaka musu kira Sagir yaleko sai yakalli bindiga karamar pistol ahannunsa yana cewa idan kuka sake kuka tada motar nan sai na fasa taya kuma dukanku bazaku tsira ba. Awwal yadan tsaya kamar bazaija motarba Netmaye yace muje mana kana ganin bindiga ne awajensa, Su Rilwan suna kallonsu ta computer sukace Awwal kaja motar mana, Awwal kawai yafinciki motar yakama Hanya shiko wancan mutumin yarinka Harbin tayar motar sai kuma yayi rashin sa'a bai sami tayarba har suka tsere masa yaciro wayarsa sannan yakira wani lamba daga bisani yakashe wayar. Suna cikin gudu over speed suka ga mutane biyu sunfito agabansu da bindigogi bisa dukkan alamu 'yan sanda ne Awwal yatako motar tsakaninsa da Allah idan kaga tafiyar dayakeyi kai kace tashi sama zaiyi, 'yan sandan nan dasuka tabbatar baida niyyan tsayawa sai kawai suka matsa gefe dayan ya hawar da bindigarsa sannan yanemi direba. Harbi daya yayi yasami Hannun Awwal, sai kawai motar tafara tangal tangal dasu, Awwal yace wayyo Allah sun harbeni, Netmaye yayi wani irin tsalle yahaye kan sterin motarsuka kara harbo wata takuma samin Awwal agefen kirjinsa yayi wani kara dakarfi aaaaaaaaa, Su Rilwan suna kallonsu ta computer hankalinsu yayi matukar tashi musamman dasukaga an harbi Awwal a kirji tashi sukayi Rilwan yayi ihu acikin gidan yayinda yadoki kujerar dake gabansa tareda kiran sunan Awwal kamar makogoronsa zata fita, yace awwwaaaaaalllll, kamar zai fadi Uziboy yarikesa suka cigaba dakallon computer din suko masu harbin sukayitayi daganan basu sake samun kowa ba, su Rilwan suka cigaba da kallonsu, sai dasuka tabbatar sun tsira sannan suka kashe computer din Rilwan yadubi Netmaye zomuje da dayan motar nan mutaresu ahanya, suka tashi cikin gaggawa sun futo bakin kofar daki Rilwan yadaga kansa sai yakalli ankov asama you are Under arrest yaji wata kalma ta fada daga wani 6angare, yayi ajiyar zuci sannan yadaga Hannayensa sama, Uzairu ma yafito akayi arresting dinsu duka, suka tsaya Rilwan yana kallo cike da mamakin yanda akayi aka kamasu, suka fito cikin korido din gidan sai ga Sadauki abakin kofa yakalli Rilwan yana yimasa dariya yana zuwa yana tafi, yana dariya sannan yace yau asiri yatonu atunaninku baza'a gane shirinku bane? Ina fada maka sannan ina tabbatar maka cewa lalle kuwa kai yarone, Rilwan yakallesa sannan yace oga kaine kuma yau silar kamani? sadauki yayi murmushi sannan yace tukunna ma bakaga komai ba ina kike my Love ahankali tabude kofa tashigo Rilwan yatashi cike damamaki yakalleta take yaji wasu Hawaye masu radadi sun fara kwaranyowa daga idanunsa, zeenat? Me kikeyi da Sadauki kua? Ashe dama tarayyar dakike dani duk makarkashiya kike shiryamin? Tadan saki dariya sannan tace wannan ai bakomai bane masoyi na ne yasani aiki kuma Alhamdulillahi nayi masa aiki yanda yadace, Rilwan yatashi haba zeenat anya kuwa kedince. uzairu dake gefe yace tabbas wannan yarinyar munafukace ina tunanin tashiga dakin bayanai dina a computer na ina gaya maka kanacemin zaiyi wuya tayi to baga irinta nan ba, dan sandan dake gefe yace kai rufemin baki idan mukaje station zakuyi bayanin. Rilwan yadubi Sadauki sannan yace oga amma wannna abin dakayi min sai Allah ya saka min. sadauki yadanyi dariya sannan yace balaifi computer gurus idan ankaiku prison zankawo muku ziyara idan nazo zan sanar daku Hanyar damuka bi muka san inda kuke, sannan kuma cewa nasan kana mamakin gani na agarin nan karka damu idan nazo zanyi maka bayanin dalilin zuwa na. 'yan sandan suka sasu agaba sun nufi mota dasu sai gasu Sagir sun dawo aguje suka iso bakin kofar suna horn. Zeenat tabude taleka Netmaye yakalleta sannan yace yauma wannna banzar tazo ko? Yace mata bude mana kofa, tadanyi dariyar mugunta sannan tanufi kofar taje tabude. Suna shigowa akayi Arresting dinsu. Sannan aka fitar da Awwal jina jina akasashi amota aka Nufi asibiti dashi.. Su kuma akayi awon gaba dasu zuwa ofishin hukumar 'yan sanda,vels / HAKAN TAKE part 35 HAKAN TAKE part 35 Posted by Bashir Sani Fesan on 08 Jan 2017 - 01:13 akan gadon asibiti dukda haka an sankama masa makulli gakuma wani dansanda wanda aka ajiye amatsayin maigadi akansa. Yadauki lokaci mai tsawo batareda yayi motsi ba likitoci suna ta kaiwa da kawowa akansa, wani matashi ne yashigo fari mai matsakaicin tsayi yana sanye da farin riga shirt colar tareda necktide a kwalarsa wani biro na makale a aljihunsa yana sanyeda wani bakin wando yayi zanzaro da wata belt mai kauri. Takalmin kafarsa sau cikine baki yasha polish sosai. Yakariso wajen tareda wasu 'yan sanda dasuke biye dashi abaya daga ganinsa zaka fahimci cewa babbane acikin 'yan sandan kasantuwar yadda suke biye dashi kut da kut. Yakariso kan gadon da aka kwantar da Awwal, tareda sallama likitocin suka amsa , rankadade barka warhaka yawwa ya amsa, haryanzu bai farfado bane? Eh ispekta haryanzu ina tunanin anya kuwa wannan zai tashi? Kamanya bazai tashiba ? Gaskiya ranka dade ayanzu haka ma ina kyautata zaton wannan yarigamu gidan gaskiya. Ispekta yayi acikin ajiyarzuci sannan yakariso inda yake yadan duba akwai alamun kaman bai mutu ba? Likitan yace eh amma fa wannan inda aka harbesa zaiyi wuya yatashi domin kuwa andanyi damage din wasu abubuwa acikinsa. Ispekta yayi ajiyar zuci sannan yace ko kunsami wani abu ajikinsa? Likitan yace Eh toh babu wani abinda muka samu sai wayarsa. Ispekta yace yawwa bani ita mugani. Likitan yajuya yakalli nurse dindake bayarsa batareda yace wani abuba tamika masa wayar yakar6a sannan yamikawa ispekta. Yabude wayar sannan yafara bin lambobi danufin ko zaiga lambar iyayensa , baiga lambar dayake bukata ba sai yacigaba da bincikawa nan yaci karo da lambar dayayi saving dashi My only 1 hakan ne yatabbatar masa dacewa wannan lambar idan bana na matarsa ba toh na budurwarsa ne. Suna kwance adaki suna nazarin karatun dasukayi amakaranta taji wayarta na Ringing taduba takalli lambarsa saita danyi murmushi sannan ta dauka tareda sallama cikin sassanyar murya. Ya amsa mata tareda cewa bashi bane. Take taji wani iri ajikinta alamun dai ba lafiya ba. Toh wanene? Yace basai na fadamiki ba amma zan sanar dake abinda yake ciki yasamu hatsari yanzu haka yana asibi sabida haka kisami iyayensa kisanar dasu kuzo kusameshi ageneral hospital daki mai lamba 13, Salati tafara dokawa yayinda ispekta bai kara jira tace wani abu ba, Aisha dake kwance da littafi ahannunta tatashi tsaye lafiya kuwa Khairat meyafaru? Tadaga kai takalleta alokacin Hawaye sunyi malale a idanunta tace yanzu aka kirani wai Awwal yayi hatsari yanzu haka yana general hospital? Innalillahi wa'inna ilaihi raajiun tafada sannan tace shikadai ne yayi hatsarin ko dukansu, Khairat tace baifadamin ba . Aisha a birkice take magana waye yakiraki acikinsu? Khairat tace bansani ba amma ina tunanin kamar likita ne ko dansanda, ajiyar zuci Aisha tayi sannan tace Allah yasa baiji rauni sosai ba sannan kuma Allah yasa shikadai ne abin yafaru dashi ba duka 'yan uwanta ba. hawaye na malale a idanunsu, suka fito dukansu suna Kiran Hajiya tafito tana fadin lafiya kuwa? Khairat tasanar da ita abinda ke tafiya gabadaya Hankalinsu yatashi kasantuwar babu wani namiji agidan babu wanda zai rarrashesu suka fito farfajiyar gidan Hajiya tasami maigadi tasanar masa sai yace toh ku kira Alhaji kufada masa mana, Hajiya tadanyi ajiyar zuci tareda fadin kaga ni nasha'afa tunanin hakan ma bai fadomin ba. Hajiya takirasa Awaya tasanar dashi sannan yace zasu iya zuwa asibitin yanzu shima zaizo yasamesu, Hajiya takira driver yadaukesu suna tafiya Hajiya tace Ina zeenat take, Aisha tayi ajiyar zuci sannan tace tunda safe tafita bamusan inda taje ba haryanzu. Khairat tace gaskiya ni fa Umma banyaba da Hankalin yarinyar nan ba bazan 6oye ba, Hajiya tayi ajiyar zuci sannan tace kyaleta idan tadawo zanyi mata magana akan yawon nan datakeyi. Gaskiya yakamata kam khairat tafada sannan tace yakamata mukira su Rilwan muji ko sun sanda faruwar lamarin. Hajiya tace dama baku kirasu kunji labari awajensu ba? Aisha ta amsa dacewa Eh. Khairat takira lambar Rilwan yashiga alokacin wayar na hannun 'yan sanda wani police yadauka tareda cewa Hello. Khairat ta kira sunan Rilwan dan sandan yace bashi bane.. Tadan sauki ajiyar zuci tareda fadin oh my God yau kam lafiya kuwa takatse zancenta da cewa da waye nake magana. Yace dan sanda ne idan kina son ganinsa kizo ofishin 'yan sanda, tace malam lafiya kuwa? Yace idan kinzo zaki samu amsar tambayarki. Yakashe kiran takara korawa da salati kuka ya kufce mata. Aisha hankalinta yakuma tashi tarike hannun Khairat tana kuka hawaye da majina suna zubo mata meyafaru Khairat dukansu sukayi hatsarin ne? khairat tace a'a kikwantar da hankalinki ba dukansu bane. Hajiya tace toh dakika kirashi me akace miki? Khairat tadan tsaya tagoge Hawayen dayagama jika mata fuska tace wai shikuma yana ofishin 'yan sanda bansan wane laifi ya aikata ba. Hajiya tayi ajiyar zuci sannan tace toh kuyi Hakuri ku kwantar da hankalinku kubarwa Allah komai insha Allahu abin zai kasance dasauki. Driver din yace Allah yakiyaye dai abinda yafaru kam yariga yafaru kukan da kukeyi din nan bashida amfani. Suka dan yi shiru amma dukda haka nitsuwa da kwanciyar Hankalin ya kauracewa zukatansu babu abinda ke zuciyarsu sai fargaba da tashin hankali , suka kariso asibitin kai tsaye suka wuce daki na 13 shiga sukayi tareda sallama hajiya ce agaba kallon 'yan sandan da tayi akansa ne yatabbatar mata cewa akwai matsala sosai su Khairat suka biyota baya. Suka kariso wajen idanun Aisha akansa tundaga bakin kofa tazo da gudu yaya Awwal katashi yaya Awwal tana faman jijjiga gadon asibitin likitan daga nesa yace you are very stupid ko kinaso yamutu ne? Dasauri tatashi takoma gefe tareda fadin a'a likita yayanane wallahi banaso yamutu. Ispekta yadubi Hajiya kece mahaifiyar wannan yaron? Hajiya tadanyi ajiyar zuci sannan tace eh toh zan iya cewa ayanzu ni nake amatsayin mahaifiyarsa kamar yadda yake alfahari. Ispekta yakuma cewa wato atakaice dai bake kika haifesa ba ? Tace kwarai alokacin Alhaji Haruna yayi sallama yabude kofa yashigo, ispekta yadaga kai yakallesa sannan yadan saki fuska tareda jiran Alhaji yakariso. Yana isowa yamika masa hannu Alhaji Haruna wannan yaron kane? Alhaji yabashi amsa kamar yadda hajiya ta amsa masa tambayar dayayi mata. Ispekta yace Alhaji Akwai matsala amma nidakai zamu tattaunata ko a gefe, Alhaji yayi ajiyar zuci sannan yace toh muja gefe bamatsala, suka dan koma gefe sannan aka kawo musu kujeru suka zauna, ispekta: Alhaji wannan yaron wane irin sana'a yakeyi? Alhaji yayi ajiyar zuci sannan yace wannan yaron daka gani dan nan garin ne amma yanzu zan iya cewa shi bakone shida 'yan uwansa agarin nan marayu ne babu irin wahalar da basu shaba daga karshe suka koma taraba suka kafa neman kudinsu acan yanzu haka ma dubamu suka zo yi. Ispekta: Alhaji zancenka hakane bashi kadai bane yana da 'yan uwa wadanda muka kamasu tare shin ko kasan wani aiki dayake aikatawa wacce takasance mummunar laifi ko da can abaya? alhaji : eh toh gaskiya nikam bansani ba, amma ispekta mesukayi haka kuma ina 'yan uwansa din ya aika masa tambayoyi biyu alokaci guda, ispekta ;ka kwantar da Hankalinka suna ofishinmu kuma mun kullesu, agaskiya laifin damuka kama yaran nan dashi babban laifine wannan daka gani bawai hatsari yayi ba. Harbinsa akayi da bindiga wanda nake kyautata zaton bazai rayu ba. Alhaji yace bindiga kuma? Sannan kana kyautata zaton bazai rayu ba? Ispekta ina zancenka yadosa kenan? dan Allah kayimin cikakken bayani yanda zan fahimceka batareda wani kace nace ba. Ispecka nan yakwashe labarin duk abinda yafaru yasanar masa , Alhaji yayi ajiyar zuci sannan yace tabbas wadannan yaran kuruciya batasakesu ba tarudesu. Sannan yayi ajiyar zuci yace ispekta wadannan yaran suna bukatar sassauci yakamata asan yanda za'ayi akashe wannan maganar harga Allah wadannan yaran anzaluncesu kafin aka gina wannan kamfanin ina tunanin sabida haka ne yasa sukeyima wannan kamfanin zagon kasa Alhaji yakwashe labarin daya faru dasu can baya yasanarwa ispekta. Abin yayi matukar bashi tausayi sannan yace Alhaji wannan case din akwai matsala sabida maigari zaishigar dasu kotu dole kotu sai ta yanke musu hukuncin gidan kaso na dan wani lokaci, shikuma wannan anharbesa ne bisa tsautsayi. Alhaji yace A'ina aka harbesa ? Ispekta yanuna masa wajen Alhaji yace lalle kuwa awannan karon nima bazan kyale ba, duk dacew wadannan yaran masu laifi ne tabbas maigari ma yana da laifi, kowa yana da hakkinsa awannan zamanin an bar zamanin da sarakuna zasu rika cin karensu ba babbaka, ispekta yace Alhaji yanzu haka idan zakayi amfani da shawarana kar ka nuna damuwanka bisa wannan lamarin insha Allahu zamu magance matsalar komai. Alhaji yace toh ispekta Allah yasa muyi nasara. Ispekta yace toh ni zantafi dama jira nake iyayensa suzo, Alhaji yace toh bari muga yajikinsa din yake Alhaji yakariso wajen yadan ta6asa babu alamar motsi atattare dashi yasa hannunsa Awuyansa duk da haka shiru baya motsawa, Alhaji shi kansa saida gabansa tafadi yawaigo yana kalle kalle suka zubo masa idanu Aisha tazo gabansa Abba meyasameshi abba zai tashi ko? Alhaji yakasa magana ispekta yaje zai bude kofa ya waigo yana kallon Alhaji tareda fadin lafiya kuwa Alhaji? Yayi ajiyar zuci sannan yace zoka dubamin wannan anya yana nan ma kuwa? Ispeka yadawo yazo yasa hannunsa akusa da wuyarsa sannan yayi ajiyar zuci yawaiga yace ina likita alokacin baya nan, ispekta yakuma cewa Alhaji saidai ayi hakuri wannan bawan Allahn yarigamu gidan gaskiya. Batareda sunce uffan ba Alokaci guda khairat da Aisha suka yanke jiki suka fadi . Cikin taimakon gaggawa aka daukesu zuwa wani daki aka daura musu ruwa. Suko Alhaji da ispekta suka dauki gawar Awwal suka dawo dashi gida sannan aka sallacesa aka kaisa makwancinsa. Su Rilwan suna sankame acikin dan karamin daki wato cell kuka kawai sukeyi. Rilwan yana kiran sunan Awwal sagir shima yana ambata kai kace zikiri sukeyi, Netmaye Uzairu dasauran mutanen suna basu Hakuri, sagir yana fadin Awwal zai iya mutuwa wannan harbin banta6a ganin wanda akayi masa irinta yatashi ba. Netmaye yace wannan bashine zancen dazakayi ba. Idan kwanan mutum yakare babu yanda aka iya sai hakan tafaru. Rilwan yace ni yanzu abubuwa dayawa suka kullemin kai. Babban al'amarin shine yadda naga Awwal rai ahannun Allah, nabiyu kuma shine yanda zeenat ta yaudareni batareda nagane cewa ita mayaudariya bace. Sannan kuma yanda akayi Sadauki yagano inda muke koda yake nasani cewa zai iya amma dole akwai wani bayanin daya samu, hmmm sannan kuma yanzu haka Asirinmu yatonu duk inda muka shiga da wannan tabon za'a rika kallonsu. Uzairu yace Rilwan kai bakon soyayya ne shiyasa zeenat tayi maka irin wannan rainin Hankalin. Ai tun daga lokacin da tace zata biyoka yakamata kagane cewa ita ba 'yar mutunci bace, yama za'ayi kwatsam na hadu da mace abariki tace zata biyoni kuma in amince ne? For what reason? Sam bazan yadda da wannan ba. Sannan kuma kana da masaniya dama ashe ita tsohuwar budurwar Sadauki ce kuma ka aminta da ita. Rilwan yace haba Uzairu kabarni da abinda yake damuna dan Allah. Sagir yace Rilwan ina tuna Awwal Audu jan wuya yace jimana wai me kukabi kuka tada hankulanku akan wannan abin ne? Bazamu wuce kwana biyu ba za'a fitardamu. Netmaye yace tunda nake wannan harkar sai yau aka kamani amma wannan karonma kawai sabida kofsawar Rilwan ne. Sam mace ba wacce za'a aminta da ita bace. Rilwan yace nifa kundameni. Alokacin wasu 'yansanda sukazo suka bude kofar suka shigo sannan suka umarcesu da fita ana bukatar ganinsu. Aka fito dasu sukaga mai gari da chairman suna tsaye gakuma Kamal agefe Sadauki da zeenat suna daga baya. Kallo daya mai gari yayi musu yaganesu. Shiko kamal yana ganin Rilwan yace Baba wancan yaron shine ya mareni rannan. Mai gari yakariso yana tafi da hannayensa good good good. Yanzu na fahimci abinda ke faruwa yadan waiga yakalli chairman yace kaga wadannan tsagerun yaran sun rikeni azuci har tunanin daukan fansaa sukeyi akaina. Chairman yace me kayi musu mai gari yace zan sanar maka anjima. Maigari yakariso kusa da Rilwan yakura masa idanu. Sannan yace yaro kagirma fa kuma dukkan sassan jikinka ta 6ullo. Yakuma duban Sagir sannan yace kaima fa yanzu wuyanka yakai yanka , sagir ya hararesa yadan kariso tareda dafa kafadarsa Sagir yasa hannunsa yature , maigari yadanyi dariya sannan yace dama nasan kai dan gardama ne. Sai dai banga dayan mara kunyar ba? Yakarisa wajensu Uzairu ku kuma banta6a ganinku ba ko ina suka samoku oho. Audu janwuya yace ranka dade idan kai baka sanni ba katambayi chairman. Maigari yawaiga yakallesa your excelency wannan wanene. Chairman sai alokacin yaganesa yafadi sunansa acikin zuciyarsa Audu janwuya sannan yakuma furtawa abayyane. Maigari kallo daya yayima chairman yafahimci tsakaninsu. yakauda kai yaciga ba da yima sauran isgilanci. chairman yadubi wani dansanda yace yaza'ayi ne acire wancan saurayi dayan yanuna masa Audu cikin rada akunnensa, dansandan yace karka damu ranka dade ai komai ahannunku yake tunda dama kune kukace zaku kaisu kotu tayanke musu hukunci. Shi saimu cire sunansa aciki sannan musauya case din yakasance sunakin mutane shida zamu shigar kotu. Chairman yadanyi murmushi sannan yace wato shi wancan saurayin yayi kokari sosai wajen satar akwatin kuri'a alokacin da mukayi za6e sannan kuma kaga yanzu haka lokacin siyasa takusa yanada matukar amfani awajenmu karmu rufeshi kuma wani abokin adawarmu yazo yaciresa. Dansandan yace ah kwarai kuwa gaskiyane ai muma nan daka gani duk 'yan sandan nan babu wanda baisan Audu jan wuya ba sabida tsabar yanda ake kawosa nan. Chairman yace toh madallah yadan kariso kusada maigari yayi masa rada akunnensa abinda suka tattauna da dansandan. Maigari yace toh ba matsala. Yanzu amaidasu cikin cell. Aka komar dasu Rilwan sannan akace shikuma Audu yatsaya. Bayan yatsaya chairman yace maigari ranka dade zaka iya tafiya. Yace toh suka fita da fadawarsa suka kama hanya, sh,. Haba Audu nazata kai nawane yakuma zakayi min haka? Audu yayi ajiyar zuci sannan yace ranka dade yau rabonka da kallona shekaru nawa? Inace tunda kukaci nasara kajuyamin fuska? Chairman yace bahaka bane kasan abin sai ahankali. Yace ni bana so kabarni nazauna tareda yaran nan sunfi min kai alheri kuma duk daren dadewa zamu fita taredasu. Chairman yace karka fadi haka mungama magana da 'yan sanda za'a cireka daga cikin wannan case din idan kai fita kuma bakayi mana adalci ba. audu yadanyi shiru sannan yace gaskiya bazan iya fita nikadaiba sabida akwai yarana biyu aciki. Chairman yadan waiga yakalli dansandan sannan yace ranka dade kaji akwai yaransa biyu shin zai iya yiwuwa duka sufita? Dansandan yayi shiru yana nazari sannan yace zaiyiwu zamu ciresu gaba daya ba matsala amma ranka dade tilas ne adan ninka mana abin goron yakarisa zancensa yana dariya. Chairman yace karka damu. Dan sandan yace jeka zanzo nasameku. Audu yatashi ko godiya baiyima chairman ba yakoma cikin cell din yasanar masu Rilwan abinda ke tafiya. Rilwan yace yauwa bamatsala zaku iya fita yanzu amma dukda haka akwai aikin dazakuyi mana. Audu yace wane irin aiki kuma? Rilwan yasanarmasa duk abinda yakeso ayimasa. Audu yace kadauka cewa angama. Jim kadan dan sandan yashigo yaciresu Audu janwuya,maaga, da dayan saurayin, suka fita ahanyar fita sukaci karo da sadauki suna shigowa shida zeenat bayan dawowansu daga yima chairman rakiya. Audu janwuya yakalleta kamar yashaketa tana kallonsa tadanyi murmushi sannan tawuce Sadauki yace ya wadannan kam sakesu akayi ne? Tace akwai alama. Suka wuce ciki Sadauki yashiga yasami 'yan sandan suka gaisa computer wizard sunanda wani dansanda yasama Sadauki kenan tunda yaga kwarewarsa wajen gano Hanyarda su Rilwan sukabi sukayi sata. Bayan sadauki sungama gaisawa ne yace inason ganin wadannan yaran, dansandan yace toh bamatsala yashiga yafito dasu wajen Sadauki yakallesu Sannan yatuntsire da dariya. Yace Rilwan bansan lokacin dakazama shahararren 6arawo Haka ba. Kodayake bazanyi mamaki ba tun lokacinda kayi kokarin nunamin cewa kaima kasan wani abu acikin wannan harkar. Rilwan yadanyi ajiyar zuci yaushe kasarnan zata gyaru wanda yake sace buhun kudi yakama dan sane mai yanke aljihu yana kiransa 6arawo? Sadauki yaciga da cewa Naga softwire dinku sannan kuma nafahimci dukkan bayanan da take aika muku. Wannan ne yatabbatarmin cewa kunyima wannan satar shiri sosai. Nasan kana mamakin yanda ka ganni awannan garin amma ba abin mamaki bane idan ka lakanci harka ta 'yan yahoo, wato shi wannan manager din kamfanin Modern Tech dakukayi cracking dinta abokina ne. Munyi karatu dashi sosai akasar indiya shi yakirani yasanar dani matsalar sannan kuma dama can inada karen farauta acikinku wato masoyiyata zeenat. Nasan baka manta zancen dana fada maka awaya ba. Zakayi dana sanin fara soyayya da ita. Shiryayyen abune tun lokacin dakake gidansu kana azumi take daukamin bayanai acikin computer dinka. Hotunanka kaf inadasu. Nina bata shawarar neman soyayyarka domin in nuna maka cewa kai karamin yaro ne kwakwalwarka bata chaji. Alokacin da zeenat ta hau computer din abokinka nanne nasamu cikakken gamsuwa gameda bayanai dinda nake bukata. Kanayimata ganin cewa bata iya komai ba. Baka san cewa idan a wannan harkar ne nima abinda zan nunawa zeenat sai dai kawai nace narigata farawa. Uzairu yakatseshi da cewa malam wai huduba kazo yimana ne ko me? Rilwan ya danyi dariya dukda takaicin dake damunsa acikin zuciya yadubi Netmaye dan Allah Netmaye siffanta min wannan bawan Allahn nasan ka gama karemasa kallo yayinda yake bayani. Netmaye yadanyi dariya sannan yace ina irin tsoffin mutane da ake zuwa kar6an tsohon tarihi awajensu. Rilwan yace eh naganesu. Netmaye yakarisa zancensa da fadin haka nake masa kallo. Suka kama yimasa dariya sadauki yadan tayasu dariya wanda bai iso zuciyarsa ba yacigaba da zance idan akayimin laifi daya Toh ina mai tabbatar maka ina daukan fansa sama da goma. Yanda kukayimin dariya yanzu zansaka kuyi kuka. Zaku koma cikin cell kuna kuka. Rilwan yace toh bismillah. Sadauki yayi murmushi sannan yace daga ganin yadda nake magana kana sauraro batareda ka fusata ba nasan cewa bakada labarin cewa dan uwanka da aka harba Allah yayi masa rasuwa, what sagir yafada yatashi abirkice yarike rigan sadauki kaine ka kasheshi din? Iye nace kaika kashesa Rilwan baisan lokacin da yayanke jiki yafadi ba shiko sagir yadamke kwalar Sadauki yaturashi jikin bango 'yan sanda sukazo suna faman 6an6aresa. Waigawar dazaiyi yakalli Alhaji haruna yarike Hannunsa yana cewa kai Sagir mehaka? Kasakeshi mana. Yana huci yarikesa yana cewa Alhaji kakyakeni da wannan munafukin. Alhaji yace mehaka sakeshi mana? Sukazo suka raba tsakaninsu. Aka maida Sagir gefe yana huruwa yana haki Sadauki yadanyi dariya sannan yace yaro kenan zakasan wanda kashake kwalarsa saika fito tukunna zanzo natareka nanuna maka nida kai da bambanci sannan yadubi zeenat yace mata muje suka kama hanya suka fita. Wani dansanda yace hey you are very stupid have you forget that you are in police station? Alhaji Haruna yarike Hannun Sagir yayinda Hawaye suka cika masa fuska yasa rigarsa yana share masa fuskar. Rilwan kuma aka daukesa aka kwantar dashi agefe aka kirawo wani likita yazo yadaura masa ruwa awajen Alhaji yazauna awajen sannan yadauki wayarsa yakira Sani yace yana zuwa. Alokacin Rilwan yafarka yakalli Alhaji agefensa Sagir yana zauna yayi tagumi hawaye sungama cikamasa idanu netmaye da Uzaru suna zauna agefe tamkar masu zaman makoki. Alhaji wai Awwal yarasu? Kalmar dda Rilwan yafara furtawa kenan bayan farfadowansa. Alokacin hawaye yagangaro daga idanun Alhaji sannan yagyada kansa alamar Eh. Shigowar Sani gabadaya suka maida hankalinsu wajensa, yakariso yadubesu yace nasan za'a rina tun kafin haka tafaru. Meyasa kuke 6oyemana dukkan halayyarku? Shin yanzu irin wannan abin da ace ataraba yafaru daku yakenan? Alhaji yakatseshi dacewa daga shigowanka sai kahau kan mutane da zance irin wannan? Yace baba nadade da fahimtar wadannan yaran ba Harka mai kyau sukeyi ba, ninayi shiru ne kawai sabida bangani da idanu na ba. Tunlokacinda sukazo cikin shekara daya har sun sayi mota kuma suna neman gidan Sayarwa nafara ko kwanto bisa aikin dasuka ce sunayi. Alhaji yakatseshi da cewa you are very stupid wai kai waya tambayeka ne? Sani yadanyi Shiru sannan Alhaji yace ina labarin su Khairat Sani yadan sosa keya tareda fadin sun farfado harma anmaidasu gida. Alhaji yayi ajiyar zuci sannan yace toh jeka idan bakada taimakon dazaka iyayi sai wannan zancen ba amfanin zuwanka. Sani yadanyi ajiyar zuci sannan yace Baba gaskiya wadannan yaran masu laifi ne sosai kuma dole ne doka tayi aiki akansu. Alhaji yataka masa birki da fadin toh naji shikenan fita kabamu waje idan hakane babu amfanin karatun lawyer din da kaje kayi. Sani baice komai ba yajuya yakama hanyarsa tafita. Alhaji yace yanzu Sani akanda katsaya kanemi mafita gara ga tafi din ko? Toh bamatsala zaka iya tafiya, yadan waigo jikinsa amace yace Baba ni banida wata hanya dazan bi ayanzu saidai idan anje kotu, Alhaji yace jeka idan kaga dama akotun ma karka shiga case din. Sani yakuma juya yacigaba da tafiya cikin zafin nama. Sagir kallonsa kawai yake cike da mamaki. A6angare guda kuma su Audu janwuya bayan dawowarsu area misalin karfe hudu na yamma, suka zauna maaga yadubi Audu yace gaskiya yakamata mushirya batun aikin da Rilwan yayi mana koma dai mu aikata aikin tun yanzu. Audu yace hakane ina mutanen area dan Allah kuzo muyi magana, suka taru Audu yace yau bayan Sallar magari ba kowa yazo wajen akwai sadakar kayan holewa. Sannan duk wani namu dake cikin garin nan kukira mana shi yazo akwai meeting sannan kar kowa yamanta yafito da barandaminsa, sukace toh bamatsala. Maaga yadubesa yace yakamata kadan basu na ta6i tun yanzu, Audu yace hakane yadauko wata jaka yaciro katon na wiwi ya raba musu sannan yace sugayyato kowane dan iska bayan mangari ba suzo. Kafin mangariba tayi tako wane mashaya labari yazaga cewa Audu zaiyi sadakar wiwi bayan Sallar mangari ba. Aikuwa wasu ko sallar basuyi ba suka hallaru awajen. Ana idar da sallar mangariba kaf aka taru sannan audu yabi kowannensu layi layi ya raba musu sai shewa suke suna jindadi. Sannan Audu yakoma gabansu yatsaya yafara bayani nasan wasu basu san dalilin dayasa nataraku anan ba. Kuma zakuyi mamaki. Toh amma ba abin mamaki bane idan kukayi la'akari da yanda shugabannin garin nan suke zaluntar al'umma baidace ace amatsayinmu na 'yan iskan gari munyi shiru ba. Yaciga ba dacewa yanzu haka bamu wuce 2 hours da fitowa daga cell ba. Ko kunsan wanda yakullemu? Chairman da maigari. Idan zaku tuna akwai wani yaro dayake zuwa nan idan yazo duk wiwi din wajenmu sayewa yake yaraba muku kyauta, suka amsa kwarai kuwa munganeshi Rilwan yace yawwa yanzu haka yana rufe acell dan uwansa kuma 'yan sanda sun bindigesa har lahira. Filin taharde da surutu Audu yace ya isa yanzu haka zamu tsaya muna gani ana wulakanta mu? Babu wanda baisan tsakaninmu da chairman ba amma tunda akayi za6e yakuke gani? Wani matashi yace haba oga kafada mana abinda zamuyi yanzu kawai. Audu yace sonake mutada zanga zanga amma bata lumana ba. Zamu kasu kashi hudu tunda munada yawa. Wasu zasuje su tsaya abakin police station anan zanga zangar lumana zasuyi. Wasu kuma zasu je kamfanin modern Tech idan sunje sai su kunna mata wuta. Sannan wasu kuma suje local govt secretariat nanma idan ansamu hanya akunna mata wuta, saura kuma su tsaya akan titi yanda babu wata motar dazata samu daman wucewa . / HAKAN TAKE part 36 HAKAN TAKE part 36 Posted by Bashir Sani Fesan on 10 Jan 2017 - 13:44 suka amsa dacewa angama oga suna shewa suna tafiya suka rabu kamar yadda ya umarcesu dayi. Dafarko wadanda sukaje station hannayensu rikeda wasu takardu masu fadi da akayi rubutu cewa . BAMAYI ZALUNCIN SHUGABANNI , ASAKE MANA MUTANENMU, ARUFE KAMFANIN MODERN TECH BAMAYI BAMAYI.. Abinda suke daukedashi kenan arubuce ajikin paper wani yatsaya agaba yana furtawa da karfi sauran wadanda ke biye dashi din kuma suna yimasa amshi. Yacigaba da tafiya. Sai da sukaje sukayima ofishin 'yan sanda kawanya tayanda babu wani dan sandan dazai iya wucewa batareda yabi ta cikinsu ba. Awannan lokacin wadanda suka tare Hanya suka kunna wuta da tayun mota akan titi takowane bangaren gari, a6angare guda kuma wadanda suka doshi kamfanin modern Tech tun kafin su iso security camera take nunawa, manager din yakira 'yan sanda yasanar musu alokacin su kuma basuda hanyar wucewa sabida wadanda ke zanga zanga suncike filin gashi kuma sai karuwa sukeyi. Harsuka kariso jikin kamfanin suka kunna ma tayar mota wuta sannan suka jefa ta ciki. Wuta tafara kamawa acikin kamfanin ahankali aka kuma jefa wani tayar itama takama takowanne 6angare na kamfanin yafara ci da wuta, Manager din sai kiran 'yan sanda yake, dayaji su shiru yakira hukumar kashe wuta sunkamo hanya suka tararda tako ina acikin gari ana kona tayu. Sai abin yakasance duk inda zasu wuce sai sun tsaya sunkashe wutar kafin su sami hanyar wucewa, acikin kankanin lokaci gari ya cakude baki daya, 'yan sanda da abin ya ishesu kawai sai suka fara harbi da bindiga bisaga umarnin da commisioner dinsu yabayar. Nanfa aka fara 6arna abin yaso yakasance yaki aka gayyato jami'an soji sannan aka bada sanarwar dokar ta6aci cikin gaggawa atashoshin yada labarai. Aka bama sojoji umarnin harbe duk wani matashin dasukagani acikin gari yana yawo. Duk wanda aka samu harbewa kawai suke,, kamal dan mai gari yaje wani waje babu hanyar dawowa gida ya ajiye motarsa awani waje yakamo hanya yana bin lungu lungu, yaci karo da sojoji daga nesa suka baza masa wuta. Yafadi awajen rai tayi halinta, andebi lokuta masu yawa ana kone kone, matasan dasuka fahimci yanda ake ta kawo agaji ma jami'an dasuke fada dasu sai suka fara warewa kawai bayan sungama tafka 6arna, wadanda kwanansu yakare anbindigesu wadanda kuma basuji basu gani ba akasari sunfi yawa aciki. Daga cikin inda aka kona akwai kamfanin modern Tech, cibiyar local govt da kuma gidan mai gari.. Dakyar aka samu shawo kan lamarin har misalin karfe 11 kafin nan gari tayi shiru daga nan hukumar kashe wuta suka samu daman shiga duk inda ake bukatarsu, suka kashe wutan gari yayi tsiit sai washe gari jami'an 'yan sanda dana soji suka kama yawatawa acikin garin misalin karfe 9 na rana aka bama kowa daman fita daga gidansa, sannan aka bada sanarwar duk wata unguwa dasuka sami gawa su tarasu awaje guda, zuwa misalin karfe 12 aka hada lissafi ankashe mutane samada dari biyarr agidan maigari ma mutane biyar suka kone yaransa biyu da kuma fadawansa su uku, akasarin gidaje an rasa rayuka sai dai daidaiku ne zaka samu basuyi asaran rai ba. Wadanda sukaji raunika ba'a iya lissafi dukkan asibitocin garin tacika da marasa lafiya. Mai gari kusan hauka yayi tsabar yanda yabirkice. Yana fama da bakin cikin rasa yaransa sai aka kuma kawo masa gawar babban dansa kamal. Alokacin shima yayanke jiki yafadi aka daukesa sai asibiti. Chairman tun lokacin daya fahimci anfara kone kone yafita ta 6arauniyar hanya yagudu tareda iyalansa. Bayan angama tarzoma aka kirashi aka sanar dashi daga bisani yazo. Yaje yasami mai gari yana kwance kamar zai mutu agadon asibiti ko magana baya iya yi. Hankalin chairman takara tashi yaciro wayarsa yakira shugaban 'yan sanda najiha yasanar yakamata yazo yaga abinda 'yan ta'adda sukayi musu agari. Ya amsa da yana zuwa. Jim kadan sai gashi nan yazo acikin asibitin yasamesu. tareda mukarrabansa. Yakariso gadon da aka kwantar da maigari mika musu hannu yafarayi bayan sun gaisa da chairman yake tambayarsa muna bukatar bayanai masu yawa gameda faruwar wannan lamarin. Chairman yayi ajiyar zuci sannan yace yalla6ai ai abinda kagani a TV da kuma abubuwan da kagani ankona nanma kadai ya isa yagamsar dakai. Ajiyar zuci yayi sannan yace nasanda wannan abinda nake nufi suwaye suka aikata wannan ta'asar? Chairman yace eh toh wannan aikin 'yan iskan yaran garin nan ne. Akwai 'yan uwansu damuka kama sunyi mana sata akamfaninmu awannan ribibin akasami akasi daya daga cikinsu yamutu ina tunanin wannan ne dalilin daya sa suka aikata wannan aikin awannan garin. Toh koma dai menene zamusan matakin da zamu dauka akai yanzu meke damun maigari kuma yajikinsa din ? Jikinsa din da sauki Chairman yace jininsa ne yahaura. Dansandan yadanyi ajiyar zuci sanann yace toh Allah yabashi lafiya, amma zan baka wata shawara karkuce zaku dauki wani mataki akan wadannan yaran da kanku. Tunda duniya tana gani kuma dukkan wadanda suka aikata wadannan laifukan kunsansu. Kwarai kuwa hakane chairman yagyada kai. Dansandan yace toh abinda nakeso kawai kubamu dama muyi aikinmu idan mungama mu mikasu ga kotu tayanke musu hukunci daidai da abindasukayi. Chairman yace toh insha Allahu zamuyi kokari kuma ku kamanta dan Allah. Dansandan yace karka damu sannan yatashi yamika masa hannu yace ni zan koma. Yafita abakin kofa yaci karo damanema labarai suna jiran fitowansa. Ranka dade mezakace akan wannan abinda yafaru jiya awannan gari? Yadanyi ajiyar zuci sannan yace toh wannan abinda yafaru dai mun daukesa ne amatsayin kaddara dukkan abinda Allah yakaddara zaifaru toh fa tilas ne babu makawa sai wannan abin yafaru. Dan jaridar yakuma cewa ranka dade kenan kana nufin babu wani mataki da hukumar 'yan sanda zasu dauka akan wadanda suka tada wannan tarzoma? Eh toh mataki kam wajibi ne mudauka sai dai bazanyi bayani ma duniya irin matakin da zamu dauka ba saidai idan mun dauka din duniya zata gani, amatsayinka na shugaban 'yan sanda na wannan yanki wane sako zaka bawa jama'a musamman wadanda suka rasa rayukan 'yan uwansu ganin cewa akasari wadanda aka kashe mutanenda basujiba basu gani bane. Eh toh sakon dazan basu da farko itace ta'aziyya ina mai tayasu takaicin rashin 'yan uwansu dasukayi Allah yajikansu ya rahamcesu sannan kuma ina mai kira garesu da suyi hakuri sujira suga irin matakin dazamu dauka akan wadannan matasan dasuka tada mana wannan tarzomar, wannan shine iya abinda zan iya fada. Dan jaridar yace toh madallah munagodiya ranka dade sai wani lokaci idan mun bukaci bayanai daga gareka zamu nemeka insha Allahu. suka sauke camera dinsu shikuma dansandan yawuce tareda mukarrabansa, su Rilwan suna cikin cell wani dansanda yashigo sannan yace musu ana bukatar ganinku, Sagir yace kaje kace bazamuzo ba. Yace kai ko kasan waye yake nemanku? Yace koma wanene bazamuzo ba. Yayi ajiyar zuci sannan yace commisioner of police ne yazo ganinku, Netmaye yace kai ba commisioner of police ba ko john kerry ne yazo nemanmu jekace dashi bazamuzo ba idan kuma za'azo afitarmu da karfi toh. Dan sandan yajuya yatafi yana kumbura baki, Rilwan yace musu kutashi muje muji kiran me ake mana, kai nifa babu inda zani Sagir yafada Rilwan yatashi yace karka damu girman kai bashi da amfani tashi muje yakama hannun Sagir yadagashi Uzairu yace yana dakyau muje. Suka kama hanya, shiko wancan dansandan yaje yasanar cewa sunce bazasu zo ba. Kafin yagama zance sai gasunan sun fito. Shugaban 'yan sandan yakare musu kallo sannan yace 'yan ta'adda ko? Rilwan yace ta'addanci kuma ranka dade ansamemu damakami ne? Yace inace kune kuka sa 'yan iska 'yan uwanku suka tada tarzoma acikin gari sanadin hakan yasa aka rasa rayukan al'umma dayawa, Rilwan yace tunda aka shigo damu nan muke zaune kuma babu inda mukaje tayaya za'a danganta ta'addancin da akayi damu idan ba wani sharrin ake nema akakaba mana ba? Dan sandan yace kana da daman dazaka fadi haka amma kusani hukumar 'yansanda ba jahilai bane yaza'ayi kunsaci kudin kamfanin maigari sanann kuma awannan hargitsin ankona kamfanin sannan kuma ankona wani 6angare na gidansa, babu yanda za'ayi ace babu hannunku aciki, Rilwan yace toh wannan kuma Allah masani mu ashirye muke da mudauki duk wani mataki da za'a dauka akanmu na satar da ake zarginmu da ita . Amma ta'addanci bamuda masaniya akai saidai muce hukumar 'yansanda tayi kokari tabinciko wannan. Commissioner yace toh koma menene idan jikinku yayi tsami zaku fadi gaskiya yacema 'yan sandan amayardasu cell, aka maidasu sannan yace akira masa ispekta sa'ad bayan ankirasa yace inaso kaje kayi bincike daga yanzu zuwa faduwar rana kanemo min sunayen yaran dasukayi kone konennan. Yace toh ranka dade angama. Sanann yatashi yafita kai tsaye majalisar su Audu jan wuya yaje yasamesu sannan yace yana son magana da Audu janwuya yatashi suka koma gefe sannan yake tambayarsa malam Audu ana zargi wasu daga cikin yaran dake zama amajalisarka da kone konen gidajen da akayi jiya, Audu ya danyi murmushi sannan yace kace kashe kashen da akayi bawai kone kone ba, anyi kashe kashe wanda kuma kowa yasani 'yan sanda da sojoji su sukayi bamuba dan ni bazan 6oye maka ba sabida nasan babu abinda zaka iya yimin, kuma zan iya shiga ko ina afadin kasar nan nasan zan fita sabida haka babu wani 6oye 6oye mune mukayi kone kone amma mu bamu kashe ko mutum daya ba. Dan sandan yadan saki murmushi sannan yace naji dadi kuma inason mutane masu fadan gaskiya irinka ko zaka iya lissafa min adadinku wadanda kuka aikata wannan aiki? Gaskiya ni bansan adadinmu ba muna dayawa idan kuma kamamu kakesonyi zan baka shawara garama ka janye idan kayi la'akari da yanda akayi kone kone akan wadanda aka rufe su 4 muka aikata wannan saika kwatanta da idan kuma ankama mutane sama da haka me zai faru Audu yacigaba dacewa nikaina bani dadin abinda yafaru jiya ba domin anrasa rayuka dayawa shawarar dazan baku gara ku gayyacemu wajenku aje mubada sheda sannan ranar dazaku kaimu kotu muje mubada sheda domin muna da hujjarmu na kona duk abinda mukaga dama? Ispekta yadan tsaya yana nazarin zantukan Audu sannan yayi ajiyar zuci yace naji zantukanka kuma na fahimceka amma yanzu abinda nakeso kasani commisioner dinmu yabani wannan case din yace kafin nan da faduwar rana yanason ganin wadanda suka tada wannan tarzomar, Audu yadanyi dariya sannan yace ka kwantar da hankalinka zanje dakaina anjima kasameni muje duk bayanin dayake bukata zai samu awajena. Ispekta sa'ad yace toh malam Audu ina godiya yamika masa Hannu suka gaisa sannan yace anjima zanzo mutafi amma kafin nan kasanarma yaranka karsuga bakanan sukuna tada wata tarzomar. Audu yakuma yin dariya sannan yace karka damu. Ispekta yajuya yatafi, a6angareda guda kuma bayan Sani yadawo gida yasami Hajiya yana bata bayani cewa Alhaji yanaso yadaurashi akan wannan case din shikuma gaskiya yanaga akwai matsala, hajiya tace me matsalar ace kana lawyer wannan abin yafaru bazaka taimaka ba? Yadanyi ajiyar zuci sannan yasauke murya tareda fadin Umma wadannan yaran 6arayi ne duniya tasheda, kuma tun farkon haduwanmu dasu Hajiya muma Sata sukayi mana idan baki manta ba dukdacewa bana nan amma nasamu labari kidnapping din Khairat sukayi shine dalilin haduwarmu dasu, sannan kuma sunce sun daina wannan Harkar sunkoma wani gashi nan kuma wanda suka afka din yanzu kiduba kigani yanda abin yazo yacakude yazamewa mutane bala'i agari. Hajiya tasauke wani sassanyar ajiyar zuci sannan tace Sani karka biyeta mutane baka la'akari da cewa wadannan yaran kanwarsu kakeso kuma ita zaka aura munshedeta da kyan hali. Yace haba umma idan kin duba ai bazaki ta6a hada Aisha da wadannan ba. Abinda nakeso ki duba da wanne idanu duniya zata kalleni ace irin wannan ta'asar da yaran nan suka aikata ni zanje natsaya musu agaban kotu da sunan karesu toh da wace hujja zan tunkari kotu? Aisha tafito daga kitchen idanunta sunyi jazur bisa dukkan alamu taji abinda suke tattaunawa. Hajiya tajuya takalleta Aisha dama kina kitchen ne. Gyada kai kawai tayi alamar eh Sannan kuka yakuma kufcemata. Hajiya tace subhanallahi Aisha meyasaki kuka kuma yanzu? Dagudu tawuce cikin daki batareda ta maidama hajiya amsa ba. Kai tsaye taje tasami Khairat acikin daki tana kwance bisa dukkan alamu itama taci kuka harta gaji tayi shiru. Kawai Aisha ta hau tattare kayanta tana hadawa ajaka. Shigowan Hajiya ne yasa khairat farkawa sai alokacin tafahimci Aisha ta shigo. Wai Aisha me kikeyi ne haka ina zakijie kike tattare kayanki. Tace Umma ni tafiya zanyi sabida naji duk abinda Hamma yafada, dama baya sona gaskiya, kafin tarufe baki shima yabude kofa yashigo cikin dakin. khairat ta tashi tarike Aisha meyafaru ne my sister? Sani yakalleta sannan yasaukar dakansa yarasa me zai kuma furtawa, Aisha tace ni gaskiya bazan iya zama da wanda bazai tausayawa 'yan uwa na ba. Sani yace kiyi hakuri Aisha yakamata ki farka idan ma mafarki kikeyi wadannan dakike cewa 'yan uwankine yanzu yakamata kidawo daga wannan zancen sabida ni aganina koda kuwa dan da nahaifane idan yazama dan ta'adda na rabu dashi kenan ballefa wannan idan kin duba zaman tare ne tsakaninki dasu uwa daban uba kowa da nasa. Dakata tadaga masa Hannu gaskiya nakosa da wadannan kalaman naka ta waiga takalli hajiya sannan tace Umma kinji batutuwan da yake furtawa ko? khairat kinaji ko? Yayunnawa yake kira 'yan ta'adda wallahi nafiya zanyi domin tun kafin nazo gidanku ina rayuwa Allah shine gatanmu babu irin wahalar da bamu jureta abaya ba. Ayanzu lokaci yayi dazakayimin gorin cewa suba yayuna bane. Mutanenda alokacin da bankai komai ba sabida su sami abinda zasu ciyar damu da kannena suke zuwa su aikata kowanne irin aiki domin su ciyar damu kake cewa ba 'yan uwana bane? Mutanen da idan ina cikin tashin hankali basuda kwanciyar hankali kake kira ba 'yan uwana bane. Mutanen da bayan sun shiga duniya sabida ni da kannenmu suka dawo, dan ni kawai Allah yayini mace? Ina da tabbacin da namiji ne ni da dukwata cakwakiya dazasu shiga tareda ne za'ayi amma duk da haka bari kagani abinda Allah zaiyi nangab. khairat tajijjigata haba Aishat wai ke a hayyacinki kike wannan maganar? Tajuya takalli Khairat tace kiyi hakuri kawata dole yau zan bar muku gida dana san yayanki haka yake da ban yadda sonshi yashiga zuciyata ba. Hajiya na tsaye tana Sauraron zantukan takasa cewa komai. Shima shiru yayi yana ta faman sake sake. Kawai ta finciki jakarta tayi waje dagudu Khairat tabiyota haba Aisha idan kika tafi agidan nan ina zakije? Tace kafin nazo gidan nan agidan lauwali nake kuma ko yaushe nakoma gidan Lauwali ina wajen zama. Khairat tace dan Allah kiyi Hakuri yayi zai tsaya musu akotun kidawo muzauna wallahi bazan iya zama agidan nan ba yanzu matukar bakya nan. Aisha tace ni dai kisakemin jaka idan bahaka ba zan kyaleki dashi khairat tadan sake kadan. Kawai khairat takuma fincikar jakar tafito saiga Alhaji abakin kofa sukayi kicibus cikin rikicewa yace Aisha lafiya. Shiru tayi takasa magana yakuma cewa ina zakije da jakarki kuma kina tafiya kina sharbar kuka? Kafin yarufe baki saiga Khairat takariso wajen ai Hamma Sani ne yace mata shi ba ruwansa da 'yan uwanta bazai tsaya musu akotu ba sabida su 'yan ta'adda ne, Alokacin sani Da hajiya sunkariso wajen Alhaji baijira wani zance ba kawai yanufi Sani yana isoshi yadaukesa da mari sai da yafadi, hajiya tazo tashiga tsakani tace haba Alhaji ya zaka dokesa haka. Cikin 6acin rai yake magana baida Hankali ne yarinya tana fama da rashin yayanta gakuma takaicin kama 'yan uwanta zai furta mata irin wadannan kalaman, hajiya tace Allah yahuci zuciyarka Alhaji bazai sake ba. Alhaji yadubeta sannan yasaukar da murya kiyi hakuri Aisha ki koma kije kizauna. Tace ni Abba tafiya zanyi gidan Lauwali yace mata kiyi hakuri kinji bazai sake fada miki haka ba. Kuma dolensa yatsaya akotu matukar yana son Aurenki idan har baije kotu ba, toh bazan ta6a yarje masa Aurenki ba, tadanyi ajiya zuci kamar zata ce wani abu sai kuma tayi shiru. khairat tazo takar6i jakar Hannunta din ta mayar sannan daki sannan Hajiya tariketa suka koma daki. Alhaji yadubi wanda yana zaune har lokacin bai sake furta wani zance ba yana rike da kuma tunsa amma kabani kunya matukar katsaya akan wannan bakan taka baka tsaya kafahimci wannan abin ba ni banga amfanin makarantar dana turaka carlifonia ba. Baice komaiba yatashi yashiga dakinsa jikinsa asanyaye yau shekaru nawa rabon Abba daya daga hannu yata6ani sai yau sabida wannan yarinyar? Tana nema ta raba tsakanina da iyayena dan na hakikancema gaskiya? Abangare guda kuma jim kadan da misalin karfe 4 na yamma ispekta sa'ad yaje yasami Audu janwuya suka je wajen commisoner. Yayi masa tambayoyi yabada amsa yanda yadace sannan comisioner yace toh kai kacancanci arufeka kafin nan aje kotu amma sabida hatsarin da zai iya faruwa . Sabida haka kaje sai ranar da zamu hadu akotu sai kuzo da duk wani wanda kuka aikata aikin taredasu. Ya amsa toh sannan Audu yatashi yatafi. Washe. Sani bayan yayi sallar asuba yaje dakin hajiya yasameta yagaisheta sannan yasanar da ita cewa shi yayi nadamar zantukan dayayi amfani dasu jiya, hajiya tace toh sai kaje kabata hakuri sannan kaje kasami mahaifinka shima kabashi hakuri. Ya amsa toh sannan yayi godiya yatashi yaje yasami Alhaji shima yabashi hakuri Alhaji yace shi ba ruwansa yayi kokari yaje yasasanta tsakaninsa da Aisha shi baruwansa. Bayan sun Karya da safe yaje yasami Aisha da Khairat suna zaune acikin dakin idanun Aisha sunyi jazur bisa dukkan alamu tasha kuka harta gaji. Yaje yadurkusa sannan yace Aisha kiyi hakuri nayi nadaman maganganun dana fadamiki jiya. Kiyi hakuri ki gafarceni kuma nayi miki alkawarin zan tsaya akan wannan shari'ar har zuwa lokacin da Allah zaisa kammala shari'ar kuma insha Allahu 'yan uwanki zasu fita kuma dukkan hakkinku da aka danne abaya insha Allahu za'a mayar muku dashi, tadanyi ajiyar zuci sannan takuma yin shiru. Khairat ta dafa kafadarta sannan tace my Sister kiyi Hakuri kiyafe masa tunda yayi nadama, tadanyi ajiyar zuci sannan tace toh naji na yafeka amma dan Allah hamma karka sake kushemin 'yan uwa kaji, yadan saki murmushi sannan yace toh Khairat bazan kushesu ba ai 'yan uwanki 'yan uwana ne. Tadanyi murmushi Khairat tace mata toh sai yanzu naga murmushi akan fuskarki yanzu ko kufa ? Sai ku cigaba da soyayyarku cikin jindadi da nishadi ance dama zaman tare sai da haka zomu zauna zomu sa6a Sani yatashi yana murmushi sannan Khairat tace Hamma yau bazaka fada bane? Yawaigo yace me ? Tace abinda kake fada mata kullum idan kunzo rabuwa, yadan sosa keya kamar bai fada ba sai kawai yace my pretty .. i forget to say that I love you, yakora da murmushi sannan khairat tawaigo takalli Aisha saura ke, tadan rufe fuskarta da gyale sannan tace I love you too.AKE novels / HAKAN TAKE part 37 HAKAN TAKE part 37 Posted by Bashir Sani Fesan on 13 Jan 2017 - 16:06 sai suka tuntsire dadariya Sani yajuya yafita fuskarsa cike da fara'a dukkan damuwan dake cikin ransa ta gushe, yakoma dakinsa yazauna sannan yafara tunanin tawane 6angare zai doshi wannan shari'ar. Cikin hanzari ya katse tunaninsa sannan yatashi yaje yashirya bayan sungama breakfast yafita kai tsaye yaje ofishin 'yan sanda yace yana bukatar ganinsu Rilwan akaje bashi iznin ganinsu, bayan sun gaisa sannan yace kuyi hakuri abinda na fada muku wancan ranar nikaina nayi nadamar hakan. Sagir yadanyi ajiyar zuci sannan yace toh bamatsala dama ni bandauki wannan abin da damuwa ba, Sani yacigaba dacewa nine zan kasance amatsayin lawyer dinku ranar daza'a gurfanar daku agaban kotu, Rilwan yadan sake daga kai yakallesa sannan yasaukarda sassanyar ajiyar zuci ahankali batareda yace komaiba yakuma yin shiru. Sani yacigaba dacewa ayau inaso naji labarinku daga farko har karshe domin kuwa hakan yanada muhimmanci sosai zai taimakamin wajen zakulo hujjoji dazanyi amfani dasu wajen kareku daga zargin da akeyi muku. Rilwan yakuma yin ajiyar zuci sannan yace gaskiya kaima Sanin kankane wannan labari ne mai tsawo amma tunda hakan yanada matukar amfani dole ne mu sanar dakai abubuwan damuka gamu dasu arayuwa daya bayan daya, Rilwan yadubi Sagir sannan hawaye suka zubo masa Sagir yadanyi ajiyar zuci yace tarihinmu bazata cika ba tilas sai mun lissafo matattun da muka rasa. Babban rashin damukayi nafarko shine rasuwar baaba Jummai wacce take kulawa damu. Sai kuma rashin damukayi nabiyu kannenmu sama da goma wadanda mota ta nikesu. Sai kuma uwa uba rashin Awwal yakafe batareda yakuma cewa komaiba. Hawaye sun cika idanunsa Sani yadan dafa kafadarsa sannan yace karkaji komai. Dukkan me rai sai ya dandani zafin mutuwa inaso kasani cewa idan kwanan mutum yakare kota wace irin hanya tilas ne yatafi. Rilwan yace hakane. Sani yace toh ina sauraronka Rilwan kai zaka iya jurewa kabani wannan labarin nafahimci Sagir yanada raunin zuciya. Rilwan yakuma sauke ajiyar zuci. Uzairu da Netmaye kallo kawai sukeyi. Rilwan yafara bashi labari daga farko har karshe. Sani yace toh madallah zanje nayi nazari akai Sannan zansan yadda zan doshi abin. Uzairu yace toh Allah yataimakemu suka amsa ameen, Sani yatashi yamikamusu hannu sannan ya fita yatafi. Aranar Zainab abokiyar Khairat kuma budurwar Sagir takawo musu ziyara kasancewar tsakiyar rana ne gashi kuma alokacin akwai zafi sabida hakane yasa suka fito cikin farfajiyar gidan suka zauna suna Hutawa yayinda suke hira, ganinta sukayi tabude kofa ahankali tashigo tana tafiya cikin kasaita gawani dogon takalminta mai tudu duk takun datayi dukkan sassan jikinta motsawa yakeyi. Aisha ta tashi tsaye tareda cewa wai wacece wancan kamar zeenat. Khairat cikin Sauri tawaiga takalleta Sannan tace banza mara kunya meyakawota gidannan ma oho. Suna kallonta tadoshi babban parlo din gidan Khairat tace ai wallahi bata isa ba. Suka tashi Aisha ce agaba suka tareta ke maciya amana meyakawo ki gidannan? Aisha ta koramata zance tadan tsaya tareda rike kunkuminta Sannan tajuya takalli Khairat yayinda take karisowa wajen, tace ni kikeyiwa gorin gida ko dayake kema gidan ubankine ko? Jitayi kamar ansara mata gatari akai tsabar yanda wannan kalmar yashigeta, cikin karfin hali tace naji ba gidan ubana bane amma dukda haka bazaki shiga ba tunda kema bagidan ubanki bane. Alokacin Khairat ta kariso wajen ita ko zeenat bata tsaya wani Sanya ba kawai tadaga hannunta ta dauke Aisha da mari. Tadafe kumatunta tareda dago kanta tace ni kika mara Zeenat? An mareki kiyi duk abinda za,,.. kawai itama taji Saukar mari akunnenta, tarike wajen tareda waigawa takalli wanda yamareta Zainab ce atsaye tace ke dan ubanki ni kika mara, zainab ta cire gyalenta tadauresa akugunta sannan tamatso tana fadin zaki rama ne? Nace zaki rama ne? Khairat tashiga tsakaninsu sannan tace zeenat tafice musu daga gida. Tace bazata fita ba saita je tadauki abinda ta manta, khairat tace ko da rayuwarki kikamanta acikin gidan nan yau saidai kimutu. Tadanyi ajiyar zuci sannan tace ai wallahi koda karfi saina shiga nadauka. Khairat tadan ja tsaki sannan tace toh bismillah ga fili ga mai doki. Aisha itako haryanzu hannunta yana dafe akan kumatunta, tafashe dakuka wallahi sai na rama marin nan, khairat tadubeta sannan tace kiyi hakuri Aisha kiyi shiru zata san tamareki yau, tadan kalli zainab tadanyi mata signal da idanu zeenat tana yunkurin shiga kawai suka rufeta da duka. Ta ko ina duka suke mata daga bakin kofa sukaji ana cewa kai kai me haka, dasauri suka waiga sukaga Sani ne yafara shigowa damotarsa ko wuce gate din baiyiba yafita daga motar yanufo inda suke aguje, bakuda hankali ne yazo yasamu sunyimata liliss har tayi laushi tana kwance tana ihu yasaka hannu yadagata Khairat tace Hamma Karuwa ce fa Kuma kakesa hannu kana rike jikinta kasan haramun ne dai ko? Yace ke rufemin baki metayi muku haka dazaku sakata gaba kuna jibga haka? Khairat tace ai kaima kasan abinda tayi mana bayan nan kuma tazo harda wanke Aisha damari. Sani yadan waiga yakalli Aisha bisa dukkan alamu idanunta sun zubar da kwalla, yakariso kusa da ita yana kallonta shatin mari yagani yakwanta akan dimple din fuskarta yadanyi murmushi sannan yace sai kika karayin kyau, nida zaiyiwu ma da zan rika biyan zeenat ta rinka wankeki da mari kullum dan narika ganin kyaunki yana karuwa, ta wani doka masa harara kamar zatayi dariya tacije tarufe fuskarta su khairat suka yimata dariya Sannan Sani yakuma juyowa ga zeenat yace mata me yakawoki gidan nan adaidai wannan lokacin? National Id card dina namanta shine nazo dauka su kuma sukace bazan shiga indauka ba. Yadanyi ajiyar zuci sannan yace Aina kika ajiye tace asaman wardrop na ajye alokacin danake kimtsa kayana daman ina shirin idan nagama zan dauka sai kuma namanta, Sani yadubi Khairat Sannan yace jeki dauko mata Id card dinta tunda kunce bakwaso tashiga muku daki, batayi musu ba takama hanya tashiga taje tadauko takawo mata takarba sannan Sani yace mata kiyi hakuri da abinda sukayi miki kinji? Tace bazanyi hakuri ba ta juya tadubesu Sannan tace zakusan kunyimin duka, saura kwana 2 ashiga kotu haryanzu maigari yana kwance agadon asibiti. Sani yagama kimtsa bayanai dazaiyi sannan yatsara masu Rilwan dukkan abubuwan dazasu fada, dukda girma da fadin da kotun takeda shi aranar kotu tacika harta batse da manya manyan baki daga cikin wadanda sukaje harda gwamna da kuma wasu manya manyan 'yan siyasa hatta sarkin musumai saida yaturo wakilinsa awannan shari'ar ga kuma 'yan jaridu ta ko ina alkalin alkalai shine wanda zai gudanar da hukunci mai gari baigama samun Sauki ba ana daddafe dashi dukda haka ya halarci kotun. Shiru akadanyi na 'yan wasu lokuta Su Rilwan aka tsaidasu a6angare guda da aka tanadarma wadanda akeyima shari'a. Wani mutumine yatashi yana sanye da riga jamfa da hula fari idanunsa sanye da farin glass wanda daga waje kana iya kallon dukkan sassan idanunsa yafara magana kamar haka: ayau ranar litinin 16 ga watan biyar shekara ta 2016 kotu zata saurari karar matasan nan 4 da ake zargi da laifuka biyu zuwa uku dafarko ana zarginsu da yin zagon kasa ga kamfanin nan na modern Tech . Nabiyu kuma akwai kutse cikin bayanai ma kamfanin modern Tech tareda satan bayanai, sannan na uku ana zarginsu da tada tarzoma acikin gari tareda konekone. Wadannan sune karan da aka shigar wannan kotun ayanzu kotun zata gudanar da wanann shari'ar sannan tayi hukunci bisa adalci yarufe zancensa din tareda zama, alkali yadanyi gyaran murya sannan yace lauyoyi sugabatar da kansu, wata kyakkyawar farar mace ce tatashe tana sanye da uniform, Sunana barista Laurat Abdallah nice lawyer din wadanda suka shigar da kara ataredani akwai abokin aikina yatashi Sunana barrista Ahmad kabir, ahankali yatashi cikin Nitsuwa sunana barist Sani Haruna, nine Lawyer mai kare wadanda ake zargi. Sannan yazauna. Alkalin yasaukar dakansa yadanyi wasu rubutu sannan yadago kansa tareda cewa acikin lawyoyin masu shigar da kara kunada tambayoyin dazakuyi ma wadanda ake zargi? Barista Laurat tatashi tareda fitowa Sarari kai tsaye taje tatsaya agabansu Rilwan , sannunku kozaku iya fadawa kotu sunakinku? Sunana Rilwan, sunana Sagir, sunana Uzairu, Netmaye yadanyi shiru sannan yace sunana mubarak amma anfi Sanina da Netmaye, sani yadanna masa harara yadan saukar dakansa sai alokacin yafahimci cewa yakofsa, tadanyi ajiyar zuci sannan tace malam mubarak kace anfi kiranka da suna Netmaye kozaka iya fadawa kotu dalilin kiranka da ake da wannan sunar? Yadanyi ajiyar zuci sannan yace Sabida kwarewa na wajen shiga Shafukan yanar gizo wannan shine dalilin dayasa abokaina suke cemin Netmaye. Tadanyi ajiyar zuci Sannan tace Netmaye ana zarginku da yin kutse acikin bayanai na kamfanin Modern Tech ko sannan kuma ana zarginku da yima kamfanin zagon kasa tahanyar satan kudadensu ko kanada daga bisani kuma ana zarginku da tada tarzoma acikin gari wanda yayi sanadiyyar mutuwar dimbin rayukan jama'a ko kanada wata zance dazaka gamsar da kotu sannan kuma da dalilinku na aikata wannan aikin? Objection ya mai shari'a zarginsu akeyi bisa aikata wannan aikin ba'a tabbatar ba sabida haka akwai kuskure bisa tambayar da barista laurat tayi hakan zaisa wanda ake zargi yarikice yafurta abinda bai aikataba Sani yakarisa zancensa yayinda yake kallon alkali. Yadan kallesa Sannan yace barista laurat ki sauya salon tambayarki, tadanyi ajiyar zuci sannan tace shin ko kanada wata zance dazakayima kotu wanda yakan iya ku6utar daku daga wannan zargin. Kafin yabude bakinsa Rilwan yace tabbas mune mukayi kutse cikin bayanai da kuma kar6an kudin kamfanin modern Tech amma tarzoma da aka tada agari mu bamuda wata masaniya akai, ta waiga tace malam Rilwan bakai aka tambaya ba kabada amsa kasani zaka iya fuskantar fushin kotu bayan laifin da ake zarginka dashi, katseta yayi da cewa objection yamai shari'a wannan laifin dukansu ake tuhuma kuma dukansu sunada damar dazasu amsa wadannan tambayoyin, tajuya tace yamai shari'a yakamata kotu tagargadi abokin aikina Barista Sani bisa shigowa lamarin tambayar danakeyi atsarin kotu idan ana shari'a ko waye akanji tabakinsa domin tantancewa da gane gaskiyar lamari tilas ne ayima kowa tambaya kuma shi din ya amsa ta, alkali yadubi Sani sannan yace barista Sani ayi hattara bisa irin wannan katsalan dan din, Sani yadanyi ajiyar zuci Sannan yazauna, takaraso zuwa wajen Rilwan da cewa kace baku kuka tada tarzoman da ake zarginku dashiba sannan kuma ka amince da cewa kune kukayi kutse cikin bayanai shin ko zaka iya gayawa kotu dalilinka na kin amincewa da tada wannan tarzomar? Rilwan yadanyi ajiyar zuci sannan yace aranar da aka tada wannan tarzomar mu muna rufe awajen 'yan sanda kuma har aka gama bamu san anyi ba yakuma za ace mune muka tada wannan tarzomar? Malam Rilwan bisa dukkan alamu kana amsamin tambayatace da tambaya shin kana nufin kacema kotu bakada alaka da wadannan matasan dasukayi wannan tarzomar? Rilwan yadanyi ajiyar zuci sannan yace kwarai kuwa. Tadanyi ajiyar zuci sannan tawaiga tace yamai shari'a idan akayi la'akari da zantukan da Rilwan yayi inaso kotu ta lura da wasu dalilai wanda zai nuna da cewa ko basu suka aikata wannan ba akwai hannunsu aciki. Sabida sunyi kutse da sata akamfanin mai gari sannan kuma alokacin da tarzomar tatashi kai tsaye suka fantama zuwa gidan mai gari suka konata tareda kamfanin idan mukayi la'akari da wannan tarzomar yana da nasaba da wani wanda yakeda gaba da maigari da kuma kamfaninsa sannan idan kotu talura babu wasu wadanda sukayi 6araka da kamfanin sai wadannan yaran da wannan nake fatan kotu zatayi la'akari takuma lura bisa wannan lamarin sannan karma kotu ta wahala wajen daukan lokaci awannan shari'ar kawai kotu tayi gaggawan yanke hukunci akan wadanda suka aikata wannan laifin. Nagode yamai shari'a sannan takoma tazauna. Alkalin yadan saukar da kansa yadanyi rubutu sannan yace Barista Sani kaji abinda abokiyar aikinka tafada ko kanada wata hujja da zaka kare wadanda ake zargi dashi? Sani yadanyi murmushi sannan yace kwarai kuwa yamai shari'a inada hujjoji yatashi yafito yakariso inda suke.. Dafarko yace inaso kotu tasake bani dama nayima wadanda ake zargi tambayoyi. Kotu tabaka dama alkali yabashi amsa, yadanyi ajiyar zuci sannan yace dafarko zanso naji kun maimaitama kotu cikakken sunakinku. Yafaro daga kan Netmaye. Yace sunana Mubarak musa uzairu adamu. Sunana Sagir sunana Rilwan. Yadanyi ajiyar zuci sannan yadubi Rilwan yace mutane biyu daga cikinku sunbada cikakken sunakinsu shin ku meyasa baku fada ba? Yadanyi ajiyar zuci sannan yace Sabida duk cikinmu babu wanda yasan ubanshi muntaso ne agidan marayu batareda munsan suwaye iyayenmu ba wannan shine dalilin dayasa iya sunakinmu shikadai muke amfani dashi. Yadanyi ajiyar zuci sannan yace Allah sarki bisa dukkan alamu wadancan su ba marayu bane kenan? Ya gyada kai eh kwarai kuwa, toh sukuma wace alakace atsakaninku dasu? Yadan kuma sauke ajiyar zuci sannan yace abokananmu ne wadanda muka hadu dasu a Taraba. Yadanyi ajiyar zuci sannan yace malam Rilwan kace bakusan iyayenku ba shin ko akwai wani danginku wanda kasani? Rilwan yace babu ni tunda nake banta6a gani wani ance yau dangina ne shi ba, barista yakuma cewa toh a ina katashi kagirma har kuka kai yanda kukedin nan. Yadanyi ajiyar zuci sannan yace atsohon gidan marayu muke wanda ayanzu haka filin ne kamfanin modern Tech take. Kace gidan marayu ada sannan kuma kace yanzu ahaka wajen ne kamfanin modern tech shin sayarda wajen kukayi ne kodai haka kawai kuka kaura awajen. Yadanyi ajiyar zuci sannan yace tadamu akayi bayan rasuwar wata tsohuwa datake kula damu akazo aka koremu aciki sanadiyyar korinmu da akayi hakan yayi sanadiyyar rasa rayukan yaranmu dayawa, shin kozaka iya fadawa mutane wanda ya tada ku daga gidan marayun? Yadanyi ajiyar zuci sannan yace alokacin maigarine yatadamu sannan kuma yayi mana korar kare sabida wai yanaso yagina kamfani awajen, shin alokacin daya tadaku yanema muku wani wajen da zaku zauna ne ko kuma kyaleku haka kawai yayi? Eh toh gaskiya zan iya cewa ma da karfin tsiya aka fitardamu domin kuwa saida yakullemu nida 'yan uwana kannenmu kuma kawai yakorasu batareda yasama musu wajen zama ba. mutanen cikin kotu suka fara salati. . Sani yadanyi ajiyar zuci yayinda Hankalin kowa yakarkata zuwa tambayoyin da akewa Rilwan yana bada amsa. Sani Yaciga da cewa inaso kayi mana bayani alokacin kun kai nawa a gidan Sannan kuma ya rayuwarku takasance bayan korarku daga gidan? Rilwan yadanyi ajiyar zuci wasu hawaye masu radadi suka gangaro daga idanunsa, munkai 15 alokacin da maigari yasa aka rufemu sabida kin amincewa damukayi da fita awannan gidan sannnan kuma yakori kannenmu daga gidan awannan ranar sunzo tsallaka titi mota tabugesu daga cikinsu yara 9 gabadaya awajen suka mutu mutanen dake wajen sune sheda, sannan kuma dama tunkafin wannan lokacin ma muna cikin mawuyacin hali domin kuwa abinda zamuci ma bamudashi gakuma wata bala'in da maigari yasake turamu aciki. Rilwan yakuma jan ajiyar zuci sannan yace Allah yasakawa lauwali maishago da Alhaji haruna sune wadanda suka taimaka mana tahanyar rike mana kannenmu wadanda suke da nisan kwana, har zuwa yanzu suna awajensu, barista Sani yadanyi ajiyar zuci sannan yace alokacin da maigari yakoreku shin meyasa baku shigarda kara kotu ta kwace muku hakkin ku ba? Rilwan yace alokacin mu yara ne Sannan kuma bamuda kudin da zamu tunkari koda 'yan sanda ne balle mushigar kara kotu. Sani yakuma cewa wato atakaice kuna da dalilin dayasa kukayima wannan kamfanin zagon kasa dukdacewa yin hakan laifi ne, Rilwan yace kwarai kuwa. Yajuya yamai girma mai shari'a duk duniya anshaida wadannan yaran marayu ne, sannan kuma anshaida inda akayi kamfanin modern Tech gidansu ne awajen. Sannan kuma anshaida irin azabtar dasu da akayi lokacin da aka koresu agidan yamai shari'a idan kotu zatayi musu adalci yana da kyau kotu tabi musu hakkinsu tukunna kafin nan azo kan laifin dasuka aikata tunda sun aminta da su suka aikata, barista Ahmad dake zaune yataso tareda fadin objection yamai shari'a tayaya barista Sani zai kawo wani batun bi musu hakkinsu yamai shari'a yin hakan kamar maida wannan shari'ar bayane dakuma 6ata lokaci tunda duniya tasheda su suka aikata wannan laifin kamata yayi kotu tayanke musu hukunci bisa laifin dasuka aikata . Yakamata kotu tagargadi abokin aikina barista Ahmad sabida wannan zance nake tsakanin ni da akai ya mai shari'a ba wai tsakanina da wanda ake zargi ba, alkali yadubesa ayi hattara barista Ahmad, Sani yakuma cewa inaso kotu tabani dama na gabatar da hujja ta tafarko wacce zata gamsar da kotu cewa wadanda ake zargi basu ne suka aikata wannan laifin ba, kotu tabaka dama, sani yace inaso kotu tabawa malam Audu wanda akafi Sani da Audu jan wuya damar fitowa. Malam Audu kalli wadannan mutanen ko kasansu? Ya kalli su Rilwan Sannan yace kwarai kuwa nasansu . Menene alakar dake tsakaninka dasu. Yadanyi ajiyar zuci sannan yace ba wani abu bane atsakaninmu illa alheri dasuke mana idan sunje majalisarmu, Yadanyi ajiyar zuci sannan yace shin ko kanada wata masaniya danganeda aukuwar wannan tarzomar da ake zarginsu dashi? Yadanyi ajiyarzuci sannan yace tabbas inada masaniya akai bazan 6oye ba sabida Nine ma jagora wajen tada wannan tarzomar. Kotu gabadaya aka zuro masa idanu take wasu surutai kasa kasa suka fara tashi acikin kotun, alkali ya buga gudumar kotu. Kowa yayi shiru, sannan barista Sani yacigaba da cewa malam Audu kace kaine jagora wajen tada wannan tarzomar kozaka iya fadawa kotu dalilinka natada wannan tarzomar. Yadanyi ajiyar zuci sannan yace kwarai kuwa inada dalilai dasuka samu tada wannnan tarzomar. Dafarko zanso mudan koma baya asali tare 'yan sanda suka kama mu da wadanda ake zargi alokacin mu bakwai ne. Kasancewar mu muna daga cikin wadanda ake jin tsoro agari masu tada tarzoma musamman alokacin siyasa shiyasa chairman dayazo yakallemu sai yakirani gefe sannan yasanar dani cewa zai fitar dani kasantuwar ina daya daga cikin wadanda suka taimaka wajen satar akwatin kuri'a alokacin da aka za6eshi. Awannan lokacin na amince suka fitardamu mu uku da yara na biyu. Bayan mun fita ne na zauna nayi tunani akan abinda akayi tabbas ba'ayima su Rilwan adalci ba gakuma dama can Rilwan yata6a bamu labarin rayuwarsu irin yanda mai gari ya azabtar dasu. Dana tuna wannan yasa natara yarana muka fita zanga zanga anan ne aka samu akasi har abin ya6aci yazama kashe kashe kuma wannan kashe kashen mubamu kashe kowa ba jami'an tsaro ne sukayita harbe mutane dasunanmu wannan shine gaskiyar lamari. Yatsaya da bayaninsa anan kotu tadanyi tsiit na 'yan dakikai, sannan Sani yace yamai girma mai shari'ah idan har ba kotu tanason wahalar da kanta bane yakamata ace kotu tagano bakin zaren wannan shari'ar sabida shi wannan matashin yafadi gaskiya koma wanne irin hukunci za'ayi masa ashirye yake daya dauka sannan kuma duniya tasheda jami'an tsaro sune sukayita harbe harbe wannan yanuna cewa sune suka kashe mutanenda suka rasa rayukansu bisa wannan tarzomar idan ma za'a kama wannan matashin da laifi baiwuce kotu ta tuhumeshi bisa laifin kone kone dasukayi agari ba ina fatan kotu zatayi la'akari da wannan sannan kuma taduba yanda aka kar6i cin hanci wajen fitarda mai laifi daga bisani ya kara aikata wani laifin nagode yamai shari'a Sannan yakoma yazauna, alkali yadanyi rubuce rubuce Sannan yadaga kansa yakalli Audu dayake tsaye a6angare guda yace malam Audu katabbata zancen daka fadi gaskiya ne kuma kana cikin hayyacinka?. Yace kwarai kuwa yamai shari'a kotu ba wajen wasa bane sabida haka bazan zo kotu nayi wasa kokuma ba ahayyacina ba. Yamai girma mai shari'a inaso kotu tabani damar yima malam Audu wasu tambayoyi barista Ahmad yafada yayinda yake tasowa daga kan kujerarsa. Yakariso sannan yace malam Audu kace chairman yafitar dakai daga hannun 'yan sanda alokacinda aka kamaku tareda su Rilwan, sannan dafarko kuma kacema kotu tsakaninka dasu Rilwan alheri ne kawai dasuke yimuku idan sun sameku amajalisa shin tayaya akayi aka kamaku tare? Yadanyi ajiyar zuci sannan yace kamar dai kullum ni mai fadar gaskiya ne wannan dalilin sabida damu mukaje muka tare motar da ake shigowa da kudi da ita ta 6arauniyar hanya mune mukeda karfin kwace wannan kudin sannan idan mun samo sukan diba mana dayawa wanda muke jindadin hakan wannan ne dalilin dayasa bazamuga ana wulakantasu mukyale ba. Barista Ahmad yakuma cewa kace chairman yafitar dakai daga hannun 'yan sanda toh menene alakarka dashi? Audu yace ai nafada saidai idan kanaso namaimaita nine mai yimasa satar kuri'a alokacin za6e dalilin fitar dani kuma sabida yakalli yanzu siyasa ta kusa shiyasa. Daga nesa chairman yake furtawa karya kake wallahi karya kake hankalin mutanen dake cikin kotun yakoma kansa yana faman hura baki yana magana, alkali yadoka guduma sannan yakoma yazauna yanata faman sam6atu, barista Ahmad yace yamai shari'a inaso wannan kotu tayi duba zuwa zancen nan wadanda aka kama sun amsa laifuka biyu sannan sunki amincewa da laifi daya kuma maifi munin sannan kuma kotu tasami wanda ya amince da wannan laifi dayan haka zalika wannan yabayyana alakarsa da wadanda ake zargi da dalilinsa na tada wannan tarzomar idan kotu talura da irin kalaman da malam Audu yayi zata fahimci cewa kama wadannan matasan shine dalilin dayasa aka tada wannan tarzomar idan kuma hakan takasance toh tabbas sunada nasaba da wannan tarzomar sukan iya kasancewa dumu dumu cikin wannan laifin dafatan kotu zatayi duba bisa wannan nagode yamai shari'a yakoma yazauna.. Alkali yadan sauke kansa yadanyi wasu rubuce rubuce na 'yan dakikai sannan yadago kansa tareda fadin.♥ Home / HAKAN TAKE novels / HAKAN TAKE part 38 the end HAKAN TAKE part 38 the end Posted by Bashir Sani Fesan on 18 Jan 2017 - 21:29 Sannan yakalli Jama'a Sannan yajuya yakalli su Rilwan na 'yan wasu lokuta sannan yafara bayani kamar Haka.�Wannan shari'ar baidace kotu ta 6ata lokacinta wajen gudanar dashi ba.�Kasantuwar dukkan laifukan da aka shigar kara masu laifin sun amsa.�Sabida haka abu mafi dacewa Shine kotu ta zantar da hukunci.�Amma kafin nan kotu tana da bukatar sanin cikakken bayani game da yaran nan,�domin kuwa koshi maraya yanada asali bawai kawai yasamu kansa bane.�Duk yanda za'ayi akwai dalilin dayasa aka kai kowannensu gidan marayun sabida haka kotu tana bukatar bincike sosai domin gano zuri'ar wadannan yaran kafin a zartar musu da hukunci.�Sabida haka wannan kotu zata daga wannan shari'ar daga yau 16 ga watan biyar zuwa ranar ashirin da uku ga wannan watan atakaice dai kotu tabada Sati daya jami'an tsaro su cigaba da tsare wadanda ake tuhuma zuwa wannan ranar kotu zata zantar da Hukunci.�Malam Alkali bari nabaka shawara karkayi kuskuren daureni ko kace arufeni domin kuwa kaga yanda yakasance da bani aka kamaba ma dubi yanda aka tada bala'i agari ina kuma ga idan nai aka kama? balle ace andaureni uwa uba ayanke mini hukuncin kisa?�Ina tausayin mutanen garin nan domin abin bazaiyima kowa dadi ba amma kuyi tunani akan wannan batun.�Alkali yadoka guduma sannan yace malam Audu waye yabaka izinin yin magana acikin kotu?�Audu yadanyi ajiyar zuci tareda zare idanu Sannan yace nidai nafada maka ne sabida kasan irin hukuncin dazakayi.�Ah toh .�Alkalin yayi ajiyar zuci sannan yace Audu dole ayimaka hukunci zaka kasance adaure har zuwa ranar da kotu zata sake zama akan wannan shari'ar.�Sannan alkali yace kotu tana Umartan Jami'an tsaro dasu tsaurara matakan tsaro sosai dukwanda aka sameshi da neman tada tarzoma akamashi arufe.�sannan kuma kotu tana gargadi ga jami'an tsaro masu kar6an cin hanci duk wani dan sanda da aka kamashi da cin hanci toh tabbas zai fuskanci hukunci mai tsanani.�Daga karshe kotu tana kira ga iyaye musamman wadanda sukeda yara matasa dan Allah ayi kokari wajen tarbiyantar da yaro ,�kar ayi wasa da kai yaro makaranta domin kuwa akasari irin wannan tarzoma da kone kone daya faru agari duk yanada nasaba da rashin karatu da kuma rashin aikinyi da matasanmu suke fama dashi.�Dafatan iyaye zasuyi amfani da wannan shawarar daga nan zamuja linzamin wannan shari'ar sai ranar ashirin da uku ga wannan watan zamu dawo muyi zaman na karshe masha Allahu.�alkali yatashi dukkan mutanen kotun suka tashi bayan yafita kowa yakama bin Hanyarsa,�Khairat da Aisha suka nufi inda su Rilwan suke suna karisawa wajensu 'yan sanda nakewaye dasu.�Aisha ,Khairat ku kasance masu hakuri da yimana Addu'a insha Allahu zamu fito kalmar da Rilwan yafada kenan. Shikuwa Sagir kasa magana yayi alokacin da ya fahimci Zainab hawaye sun jika mata fuska.�Basuce koda Uffan ba 'yan sandar suka wuce dasu Rilwan.� Hajiya tazo takama Hannun Khairat da Aisha tajasu tace mekukeyi haka kuzo mutafi insha Allahu zasu fito.�Washe gari da Safe ispekta Sa'ad ya sammaka zuwa wajensu Rilwan da tambayoyi .�Shin babu wanda kuka Sani koda yata6a nuna muku cewa yasanku awani waje? �Rilwan yace tunda nayi wayo nasamu kaina ina gidan marayu Baaba Jummai kadai nasani bansan kowa ba.�Yadanyi ajiyar zuci sannan yace kaifa Sagir? �Sagir yace nima haka babu wanda nasani Sai Baaba jummai.�Ispekta sa'ad yakuma cewa tunda kuke da ita Baaba jummai din ko akwai wani labari tada ta6a kawo muku wanda yakeda nasaba gameda rayuwarku?�Sagir yadanyi ajiyar zuci Sannan yace gaskiya babu amma kafin ta rasu alokacin da tafara jinya tace akwai maganar datakeso muyi saidai jinyarta ya hanamu samun daman dazamu zauna har muyi wannan maganar,�ispekta yadanyi ajiyar zuci Sannan yace.�Ancemin kunada kanne wadanda kuka kasance taredasu agidan shin ayanzu guda nawa ne suka rage kuma a ina suke da zama? �Rilwan yace su 3 ne suka rage matabiyu da kuma namiji daya babbar cikinsu tana zaune agidan Alhaji Haruna Sauran kuma Suna zaune agidan lauwali maishago dake kallon kamfanin modern Tech.�Ispekta yadanyi shiru sannan yace shin alokacin da aka koreku daga gidan marayu shin babu wata kungiya takare hakkin bil Adama datayi yunkurin kar6a muku hakkin ku? �Rilwan yace gaskiya babu asali ma duk wanda muka kaimasa kukanmu sai ya banzatar damu,�intakaicemaka limamin masallacin jumma'a yayi iya bakin kokarinsa wajen nema mana taimako amma abin yacitura wannan shine babban dalilin dayasa muka dau alkawarin neman kudi takowane hanya.�Ispekta yayi ajiyar zuci sannan yace madallah sai ku dauki wannan kaddarar ku kasance masu hakuri da abinda zai faru sannan ku kar6i duk hukuncin da kotu zatayi muku hakan zaisa abin yazo muku da sauki.�Rilwan yace mungode ispekta yatashi sannan yace karka damu.�Ispekta Sa'ad yafita kai tsaye yanufi gidan maigari haryanzu yana fama da jinya Ispekta yakariso inda yake bayan yayi gaisuwa sannan yanuna masa id card dinsa yasanar dashi cewa shi jami'in tsaro ne yazo zaimasa wasu tambayoyine gameda karar dasuka shigar,�mai gari yadan taso ahankali ya kishingidu akan pillow sannan ya umarci dogaransa dasu basu waje,�ispekta yace ranka dade da farko ina mai jajanta maka da kuma yimaka ta'aziyyar rashi dakayi na danka Kamal dakuma Sauran mutanenka fatan Allah yajikansu yayi musu rahama.�Mai gari yace ameeen.�Sannan Ispekta yacigaba dacewa ranka dade inaso ka kasance mai hakuri bisa tambayoyi dazanyi maka yadanyi ajiyar zuci sannan yakuma cewa karka damu yi aikinka.�Ispekta yace wace irin alakace tsakaninka da wadanan yaran da ake zargi?�Gaskiya ni banida wata alaka dasu yafada yayinda yake tari ..�Ispekta yace masa Sannu .�Sannan yacigaba dacewa bisa shedu da kuma zahirin zantuka ka tadasu daga gidan marayu shin menene dalilin tadasu dakayi din? �Maigari yakuma yin tari da kyar yatsaya sannan yace wannan kuma wace irin tambayace? �Ispekta: ranka dade dama nacema saidai kayi hakuri da tambayoyin da zanyi ma.�Maigari: wadannan yaran asalinsu ba 'yan nan garin bane rana tsaka aka kawosu domin kuwa alokacin da aka kawo yaran nan nayi iya bincikie bansamu asalinsu ba.�Wata tsohuwa dasuke tareda ita na tambayeta tace itama wani mutumi ne yabata ajiyarsu na rana 1 daga wani kauye dake kusa da iyakar Najeria da kamaru nan yabata su, tunda mutumin yatafi tace bai kara dawowa ba,�ita kuma sai fada yatashi agarinsu shine tagudo dasu takawosu wannan garin daga nan tafara saida tuwo tana samu tana ciyar dasu wani lokaci harma abinci nima nake kai musu nasayama yaran nan buhun shinkafa yafi a kirga. ispekta yadanyi ajiyar zuci sannan yace toh ya akayi gidan marayu yashiga Hannunsu Sannan kuma daga baya aka tadasu agidan?�Maigari: eh toh tsohon dan majalisar wakilai Alhaji Bello marigayi shine ya gina musu gidan alokacin da yasameni yasanarmin zai gina gidan marayu harda makaranta zaiyi musu aciki na amince masa da hakan sannan nabashi fili batareda yabani ko sisi ba haka aka gina gidan sannnan kuma alokacin da gidan nan yashiga Hannunsu ma acikin wadannan yaran babu wanda yakeda wayo,� Shiyasa basu san alherin danayi musu ba.�Ispekta yace toh ranka dade kakoresu haka kawai meyasa baka basu wani gidan dazasu je su zauna ba?�Maigari yayi tari sannan yace yakake wannan tambayar ne?�Wannan garin kam ba gari na bane?�Komai nacikin garin nan akarkashin ikona yake.�Sabida haka ai nayi musu adalci da na kyalesu agarina ma sabida babu wanda yasan asalin yaran nan waya sani ma ko shegu ne su?�Ispekta yadanyi ajiyar zuci Sannnan yace toh ranka dade nagode kuma nizan tafi dan naga kana fama da jinya Allah yabaka lafiya.�Ispekta yatashi yafita sannan dogarawan Maigari suka dawo.�Ipekta bayan yafito yadan tsaya yana tunani hmmm gaskiya wannan azzalumin mutum ne.�Amma zuwana wajensa yayi amfani koma mene naji cewa asalinsu daga iyakar najeriya da kamaru suke duk da cewa bai fadamin sunan garin ba.�Yakatse tunaninsa cikin hanzari sannan yashiga motarsa yana tafiya yana sake sake gaskiya aikin nan yamin yawa kyanta in nemi wani, amma kuma wani zai iya dagulamin lissafi domin kuwa akasari 'yan sandanmu cinhanci ya6atasu hmm gaskiya gara nayi iya bakin kokari na kozan samo bakin zaren.�Kai tsaye gidan Alhaji Haruna yaje bayan yayi parking sannan yashiga kai tsaye yayi Sallam afalo Sani yafito da wani paper ahannunsa ganinsa ne yasa ya karaso da murmushi hahh ispekta sa'ad barka dazuwa ,�ya amsa bayan sun gaisa sannan yasanar dashi bayanan daya samu sannan yace yanason ganin Aisha,�Sani ya kirata awaya jim kadan saigata tazo ,�bayan sungaisa da ispekta sannan yasanar da ita cewa yazo ne yayi mata wasu tambayoyi.�Tace ashirye take data bada amsa,�ispekta yafaradacewa bisa binciken danayi nasamu cewa kun tashine gidan marayu ahannun wata mata dakuke kiranta Baaba jummai hakane? �Tagyada kai tareda dace eh hakane.�Ispekta yacigaba dacewa sannan kuma bisa binciken danayi duk 'yan uwanki babu wanda yafi shakuwa da ita wannan matar kamarke zai iya yiwuwa ita wannan matar tasan asalinku takan iya yiwuwa ta ta6a baki labari gameda ku? �Aisha tadanyi ajiyar zuci Sannan tace eh toh gaskiya tunda muke tare da Baaba jummai bata ta6a bani labari daya danganci asalinmu ba sai dai kafin tarasu tace akwai wani zancen da zamuyi amma harta rasu bamu samu daman yiba sabida jinya datake fama dashi,�yace toh abinciken danayi nasamu cewa kunzone daga bakin boarder tareda ita wannan matar,�sai dai bansamu cikakken sunan garin ba.�Tadanyi ajiyar zuci sannan tace toh bamamaki hakan ne amma nikam dai bata ta6a fadamin ba.�Sani yana gefe yadanyi ajiyar zuci Sannan yace ispekta Sa'ad wato gano asalin wadannan yaran zaiyi matukar baka wahala.�Yanzu haka mukaddara kasamu makama daya suna bakin boarder tsakanin najeriya da kamaru wannan ma bakada tabbacin Hakan ne.�Idan fa zaka tsaurara bincike ne toh fa tilas ne kaje can iyakar najeriya dakamaru kayi bincike.�Kuma shin ko kasan garuruwa nawa zaka samu abakin boarder? �Kauyuka nawa ne.?�Zaka samu? �Kuma sanin kankane akwai fadace fadace awancan wajen wasu 'yan kamarun suna fada da 'yan najeriya matukar ka tsallaka cikin yankin dasuke amatsayin dan najeriya toh fa abinda zai rabaka dasu sai dai Allah yakiyaye.�Ispekta yadanyi ajiyar zuci sannan yace wato barrista ni ba wannan bane damuwata.�Babban abinda ke damuna shine rashin inganta tsaron nan da commisioner yayi sannan kuma bai bada karfin gwiwa wajen nemo asalin yaran nan ba kamar yadda alkali yafada,�sannan kuma kaduba kagani ni kadai aka bari akan wannan case din.�sani yadanyi ajiyar zuci sannan yace balalle bane asamu yanda akeso balalle bane kotu tasamu cikakken bayanin datake bukata,�kawai abinda zakayi idan kaga wannan bazaiyuba kayi kokari kasamu wata hujja dazaka kai kotu wacce zata iya maye gurbin wancan.�Ispekata yadanyi ajiyar zuci sannan yace bana tunanin akwai wata hujja dazata fito mai muhimmanci a kotu kamar kawo iyayensu nan dazanyi amma zanyi dai iya bakin kokari na.�Sani yadanyi ajiyar zuci sannan ya ispekta dazakabi shawara na da kahutar dakanka.�Idan anje kotu za'ayi maka tambayoyi akan hujjar da aka nema awajenka.�Abinda nakeso dakai kawai kanunawa kotu cewa kayi iya bakin kokarinka baka samu cikakken bayani gameda asalinsu ba,�sai kuma kayi kokari kakawo wani hujja akotu nadaga laifinsu ko kuma zaluntarsu da akayi.�Isekta yadanyi ajiyar zuci sannan yace toh bari dai zan zauna nayi tunani akan wannan zancen.�Ni kadai aka hada da aikin Sani yadanyi murmushi tareda cewa ispekta kenan.�Sabida rikon gaskiyarka ce tasa aka za6eka amatsayin wanda zaiyi wannan aikin kai kadai dalili kuwa ansan sauran basu kyale cin hanci sai sun kar6a Ispekta yadanyi dariya yayin dayatashi tsaye barista Sani kenan nizantafi.�Sani yace toh amma nima inaso natambayeka Wani abu.�Ispekta yace toh bamastala yakoma yazauna akan kujerar.�Sani yace inaso kayimin bayani cikakken tawace Hanya 'yan sanda ku kabi aka kama wadannan yaran?�Yadanyi ajiyar zuci sannan yace alokacin da manager din kamfanin maigari yakawo mana karar anyi musu 6arna akamfaninsu mai yawa sannan kuma anyi musu kutse acikin computer.�Bandauki case din amatsayin babba ba amma ganin yanda suka damu da abin yasa muka tsaya.�Sannan kuma shi manager din kamfanin yanada wani aboki wanda yakeda zama ataraba Sunanshi Sadauki wanda yakasance masani ne sosai akan Na'ura mai kwakwalwa sai yakirasa yazo da taimakonsa yagano wata softwire datake aika musu da bayanai.�Yadanyi shiru sannan yaci gaba dacewa alokacin bamu tabbatar dasu ne ba sai da wata yarinya da take taredasu ina tunanin budurwar daya daga cikinsu ne,�haka ta aiko mana da bayani cikin kankanin lokaci taturo mana Address din gidan.�Bayan ta turo saida mukayi bincike sannan muka tabbatar dacewa Su dinne kuma haryanzu suna kan samun bayanai gameda kudaden da suke shigowa.�Sai mukayi tunani sannan muka yanke shawarar ajiye bayanai acikin computer din wanda zai nuna cewa za'a kawo wani kudi ta 6arauniyar hanyar.�Sabida munsan duk abinda yake gudana acikin computocin kamfanin Modern Tech kusan agabansu akeyi.�Yacigaba da cewa dalilin dayasa mukabi wannan hanyar kuma so muke mukamasu dumu dumu cikin wannan laifin bayan mun ajiye bayanai mun tura .�Daga bisani muka bada umarnin aturo wata mota da kudi tareda jami'an tsaro biye dasu bayan mungama wannan shirin sai aka tura wasu 'yan sanda suka tsaya abakin gari sannan wasu kuma suna biyeda wancan motar.�Anan suka tare wancan motar suka kwace kudin ahanyar dawowa suka cikaro da 'yan sanda wadanda sune dasukayi yunkurin arcewa sai wadannan 'yan sandan suka harbesu anan aka samu tsautsayi direbansu aka harbesa kaji dalili kenan,�sukuma kafin su dawo ankaiwa gidan dasuke farmaki aka kama wadanda ke tura musu bayanai tacikin na'ura mai kwakwalwa.�Sani yadanyi ajiyar zuci Sannan yace shin ya akayi budurwar dasukazo da ita daga taraba har kukayi nasarar hada kai da ita wajen kamasu? � Ispekta yace eh toh wannan kuma ita wannan yarinyar 'yar tarabace kamar yanda mutumin dayayi mana aikin kamasu a computer shima dan taraba ne.�Sannan dama can shi wannan mutumin maigidan daya daga cikinsu ne da ake kira Rilwan.�Bayan sun Sami matsala acan sai Rilwan yaje yanemi budurwar wancan shi Sadaukin kenan.�sani yace nafahimta cigaba inajinka.�Yaci gaba dacewa ita kuma sai tanuna tanasonsa alhalin basonsa take ba.�Har yakasance Rilwan baya 6oye mata dukwani sirrinsa alhalin baisan basonsa takeyi ba.�Ita Sadaukin takeso amma haka tayita juya hankalinsa Har takaiga zai iya zuwa da ita ko ina ahaka ne dasukayi batun zuwa nan ita kuma sai tayimasa batun zata rakosa yagabatar da ita anan wajen 'yan uwansa amatsayin matar dazai aura wannan shirin sunyi ne da sadauki tun kafin susan da cewa ga abinda zai kawo su Rilwan gari.�Bayan sunzo ne yarinyar ta fahimci abinda yakawo su sannan ta sanarma Sadauki.�Sani yadanyi ajiyar zuci sannan yace .�Toh lalle kuwa wannan batun yayi abu sai kace wanda aka shiryashi afilm.�Ispekta yadanyi dariya .�sannan yace amma zanso naje nakalli irin bayanai dinda suke sata Sani yafada yayinda yatashi tasye ispekta yana faman tafiya .�Ispekta yace eh toh zaka iya amma matsalar bazaka samu gamsassun bayanai ba Sabida duk computocin kamfanin modern tech din sun kone sanadiyyar.�Tarzomar da akayi din nan.�Sani yace oh my God amma ai akawai computer din yaran tana ina?�Ispekta yace sunada laptop guda biyar suna ofishin mu idan kana so zamu je nabaka sai mu kara bincike akai.�Sani yace yawwa abinda nakeso muyi kenan yanzu anjima zanzo insameka .�Ispekta yace toh badamuwa sai kazo yatashi yamika masa hannu sannan yafita.�Aisha tayi ajiyar zuci sannan tadubi Sani tace kanajin irin zantukan da wannan mutumin yake fada akansu?�Sani yace karki damu sai nayai bincike akai tukun na.�Sani yaje yayi wanka sannan yatafi ofishin 'yan sanda yasa i ispekta sa'ad suna dauki na'urorin suka shiga dakin bayanai din.�Bayan sungama gani Sani yace wannan babbar hujjace dazan gabatar akotu amma kaine zan kira ka zo kabayar da sheda dabakinka.�Ipekta yace toh badamuwa.�Ayau ashirin da uku ga watan biyar ranace da kotu zatayi zaman karshe bisa wannan shari'ar.�Kotu tacika fiyeda wancan.�Bayan alkali yashigo magatakarda yagama bayani sannan.�Alkali yafara bayani kamar haka kamar dai yadda muka tsaya awancan ranar kotu ta umarci hukumar 'yan sanda data binciko asalin wadannan yaran Sabida haka ina fatan 'yan sanda sunyi nasarar gano wannan abinda kotu ta bukata daga garesu sabida haka kotu tana bukatar 'yan sandan da aka daura akan wannan binciken dasu fito suyima kotu bayani.�Ahankali ispekta Sa'ad yafito Sannan yafara bayani kamar.�Agaskiya samo asalin wadannan yaran bakaramin abu bane kasantuwar babu wanda yaji ko yataba samun labari, hukumar 'yansanda tayi kokarinta wajen zakulo 'yan uwan wadannan yaran amma abin yacitura sabida haka muke bama kotu hakuri bisa wannan rashin nasarar samun bayanai damukayi.�Alkali yadan sauke wata sassanyar ajiyar zuci sannan yace ispekta abinciken dakayi banda wannan babu wani bayani daka samu? �Ispekta yace akwai .�Alkali yace toh kayi ma kotu bayani gameda wannan.�Yafara bayan munsami sirrin bayanai cewa kamfanin modern Tech bana maigari kadai bane kamfanin hadin gwiwa ne dashi da chairman.�Sannan kuma munsamu bayanai cewa kudinda wadannan yaran sukabi bakudin wannan kamfanin bane kudi ne nakaramar hukuma wanda ake warewa domin biyan ma'aikatan karamar hukuma salary tanan ne ake bin 6arauniyar hanya da kudin ana zuba su ajarin kamfanin modern Tech.�Wasu kana nan surutai suka fara tashi sannan alkali yabuga guduman kotu daga sannan akayi shiru.�Mai gari alokacin yana kwance sai yafara tareda tun yanayi ahankali har yafarayi dakarfi dogarawansa suna rike dashi.�Yamai girma mai shari'a inaso kotu tabani damar yima ispekta Sa'ad tambaya barista Aisha tafada.� .anbaki dama sannan tatashi tafito tadubesa ispekta sa'ad kayi kokari wajen wannan binciken toh amma tayaya za'ayi kotu tagamsu da bayananka alhalin bakayima kotu cikakken bayanin hanyar dakabi kasamu wadannan bayanai din ba?�Yadubeta sannan yace munsami wadannan bayanai din acikin computocin wadanda ake zargi idan kuma kotu tana bukatar ganin wadannan bayanai din nazo da na'urorin nakan iya daukowa nabude wajen da bayanai din suke sannan kowa yashaida,�tadanyi ajiyar zuci sannan tace ispekta basai ka kawo mana mungani ba koma menene amma dukda haka wadannan yaran sunkasance masu kutse acikin na'urorin jama'a kuma dama can sun riga da sun amsa laifin da kotu take tuhumarsu akai da wannan nake fatan kotu zatayi gaggawan yankewa wadannan yaran hukunci daidai da abinda suka aikta.�Sannan takoma tazauna barista Sani yafito ahankali yakariso inda ispekta yake tsaye sannan yace kayi kokari sosai amma yanada kyau kagabatar ma kotu dukkan abinda kasamu domin gamsar da ita.�Ispekta yayi ajiyar zuci sannan yace hakane.�sani yace yamai girma mai shari'ah inaso kotu tabani damar gabatarda wadannan bayanai din.�Kotu tabaka dama aka dauko computer din sannan aka budeta aka hadata da wani babban tv wanda kusan dukkan mutumin dake cikin kotun yana ganin rubutun dake gudana aciki.�Sannan barista Sani yadubesa yace ispekta kanunawa kotu wadannan bayanai din.�Ispekta yashiga wajen wannan shine salaryn watan data gabata yabankado bayanai gabadaya.�Kowa yana gani ,�alokacin maigari taari takufce masa har jikinsa ta mace.�Sannan alkali ya umarci da a fita dashi zuwa asibiti.�Ana cikin wannan batun saiga wani dattijo yashigo karfaffa da farin gare yanada dan tsayi yana tafiya wasu mutane masu bakaken kaya da kuma wasu sojoji biyu suna mara masa baya yashigo cikin kotun kai tsaye,�alkali yace malam yadai zaku shigowa mutane kotu batareda izini ko sallama ba.�Wannan dattijon yadanyi murmushi sannan yace ina fatan kotu zatayi mana afuwa bisa wannan kuskuren.�Yacigaba dacewa inada batu akan case din da ake gudanarwa din nan ne.�Alkali yadanyi ajiyar zuci Sannan yace muna Sauraronka.�Yafara dacewa sunana laftanal kanal Idris bukar mai ritaya.�Nakasance mai neman yaran da ake gudanar da wannan shari'ar akansu sama da shekaru goma.�Alkali yadany ajiyar zuci sannan yagyara zama dukkan lauyoyi suka koma suka zauna suna Sauraronsa.�Alkali yace munaso kayi mana cikakken bayani yanda zamu fahimceka.� �Yadanyi ajiyar zuci sannnan yafara dacewa shekaru goma shabiyar da suka wuce alokacin ina matsayin jagora na rundunar sojoji wadanda suke aiki a iyakar najeriya da kamaru.�Ispekta Sa'ad yadanyi ajiyar zuci sannan yazubawa wannan mutumin idanu.�Yacigaba dacewa alokacin ayankin ana fama da barayi dakuma 'yan ta'adda sabida haka ne yasa muke aiki awajen. �Awani Kauye da ake kira Dambore dake iyaka alokacin ansamu wasu 6arayin Shanaye dasuke zuwa sukashe makiyaya daga bisani sukwashe shanayensu,�alokacin akwai wani 6arawo daya addabi mutane yakan kashe makiyaya ya kwashe dukiyoyinsu da matayensu dakuma yaransu,�alokacin muka kaima wannan 6arawon farmaki nan mukayi nasarar kashe wannan 6arawon sannan muka kwashe dukkan mutanen daya tattara dakuma dukiyoyinsu Sannan muka dawo dasu dukkan kauyukan dake kusa da wajen kusan dukkan mutanen munsami 'yan uwansu sai wadannan yaran sune muka rasa 'yan uwansu,�alokacin ina fama da barazana sosai musamman wajen wanzar da zaman lafiya sabida haka yasa na damka wadannan yaran ahannun wani malami wanda shi wannan malamin yayimin alkawarin rike wadannan yaran har zuwa ranar da na dawo nabukaci ganinsu idan kuma Allah yabayyana iyayensu zai basu 'ya 'yansu.�Ahaka mukayi yarjejeniya dashi.�Tun daga wancan lokacin nikuma natafi da rundunata aka turamu kasar laberiya mukaje wanzar da tsaro sai ashekarar data gabata muka dawo alokacin nabukaci ritaya.�Bayan nayi ritaya sai nafara tunanin ayyukan danayi yayin danake soja.�Acikin wannan tunanin nafada cikin kogin tunanin wadannan yaran tundaga wannan ranar bana iya yin bacci sannan kuma koda yaushe idan nakwanta koda nayi baccin sai nayi mafarkin ga wadannan yaran suna bukatan taimakona acikin mafarkin..�Wannan shine yasa nafaraji ajikina cewa duk inda wadannan yaran suke suna cikin mawuyacin hali na bukatan taimako.�Tundaga nan nafara nemansu yayinda nafara zuwa wajen malamin dana mika masa amanarsu koda naje sai natararda wajen ya sauya babu alamar tsangaya balle nakalli almajiri awajen nayi tambaya aka cemin ai wannan malamin shekaransa goma sha daya da rasuwa.�Haka nayi musu ta'aziyyarsa sannan natambayesu batun wadannan yaran.�Daga nan suka sanar dani cewa akwai wata mata wacce suka hadu da ita alokacin da 6arayi suka kawo musu wani farmaki bayan kashe babbansu da akayi awancan lokacin ne Allah yayima Malam rasuwa itako wannan matar tadauki wadannan yaran tatafi dasu amma babu wanda yasan inda tashiga dasu amma ana kyautata zaton tashigo cikin wannan kasar dasu tabar bakin boarder.�Nayi musu godiya sannan nadawo gida duk da haka bandena irin wadannan mafarkin ba.�Hakan yasa hankalina yakuma tashi.�Nakuma tashi shiga neman wadannan yaran iyalai na sunkasa gane me nake ciki tunda nayi ritaya wasu suna tunanin cewa ritayar danayi ne tasa nakoma irin haka.�Na koma ga Allah namika masa komai dare rana banida Addu'ar data wuce ta wadannan yaran.�Alhamdulillahi Allah ya amsamin nakama tashar NTA ina gani sai Allah yasa naji inda alkali yake batun kotu tadaga wannan shari'ar zuwa sati daya inda kotu ta umarci 'yan sanda dasu binciko asalin wadannan yaran danayi tunani nafara lissafi jikina yabani cewa wadannan yaran sune wadanda nake nema. Duk dacewa bani da tabbas amma hakan nakamo hanya daga benue zuwa Adamawa bayan nazo nafara bincike gameda lamarin na hadu da wani bawan Allah wanda yabani masauki yayinda nazauna akofar shagonsa nahuta.�Bayan nagama hutawa nake tambayarsa nan yazantar min da komai Sannan yacemin tabbas wadannan yaran yayi musu farin Sani domin kuwa yanzu haka sauransu ma suna gidansa,�naji dadi sosai danaji wannan batun daga bisani na bukaci daya kaini gidansa bayan munje yanunamin yaran guda biyu naji dadi sosai dana kallesu yayinda naga yaran sun girma sosai ina tunanin sune mafiya kankanta acikin yaran su biyumace da namiji suka cemin sunakinsu Bilal da fatima.�Naji dadi wanda bazai misaltu ba.�Hmmmmm batareda na 6ata lokaci ba yayimin kwatancen wannan kotun mukazo nida masu yimin rakiya domin ganinsu shiyasa nazo wannan shine cikakken bayanin danake tafe dashi.�Yatsaya anan Rilwan , Sagir suka zuba masa idanu kasantuwar basu ta6a ganinsa ba amma azuciyarsu dasukaji bayanansa tabbas sun fahimci cewa alabarin dayazo dashi gaskiyace.�Kotu tadanyi tsitt.�Alkali yadanyi ajiyar zuci sannan yace kanal idris mai ritaya kotu taji bayananka sannan kotu ta gamsu dasu shin yanzu zuwanka kotu kazo ne amatsayin wanda zai tsaya musu matsayin iyayensu ne ko dai kazo sanar damu asalinsu ne?�Yace mai shari'a kenan nazo ne amatsayin mahaifinsu nine nan zan tsaya musu nakuma ji dukkan laifukan da aka kamasu dashi amma inaso kotu tayi la'akari da irin halin da suke ciki yayinda suka aikata wannan abin.�Objection yamai shari'a wannan mutumin yazo kuma yanaso yashiga hurumin kotu sabida haka yakamata kotu ta taka masa birki bisa lamarin dayake kokarin shiga domin kuwa batun dayazo da ita ta gamsar dakotu dama wannan yana daya daga cikin bayanin da kotu take bukata kuma kotu tasamu babu abinda yafi cancanta sai kotu tayanke hukunci barista ahmad yafada yayinda yakatse dottijon da zance.� Mai shari'ah yadanyi shiru sannan yace acikin lawyoyi ko akwai wanda yakeda magana ko tambaya dazaiyi?�Duka sukayi shiru sannan alkali yadanyi wasu rubutu daga bisani yadaga kansa sannan yace godiya ta tabbata ga Allah dayakawomu karshen wannan shari'ar �dafarko wannan kotun zata farayin kira ga jama'a musamman shugabanni ku kula sosai bisa hakkin maraya tabbas antauye hakkin maraya awannan gari tamu an wulakantasu ankuma tozartasu alokacin da yadace ataimaka musu.Alokacin da suke bukatar abinda zasuci kawai alokacin aka kara tozartasu tahanyar tadasu daga gidan dasuke.Awancan lokacin sun nemi taimako awannan garin amma basu sami wanda zai taimaka musu ba,awancan lokacin har Limamin masallacin jumma'a naji yana nema musu taimako ina cikin wannan garin ni kaina amma ban iya taimaka musu dakomai ba.Shin kuna tunanin Allah zai kyalemu hakane?Mun zuba idanu muna kallonsu bama su kadai ba marasa karfi suna nan birjig agari wasu sunabin lungu lungu suna neman abinda zasuci.Wasu kuma har watsarwa sukeyi shin kuna tunanin Allah zai kyaleku?Kutada su daga gidan marayu batareda kun basu mafaka ba daga bisani bala'i tafaru agarinku sannan kuma ku dangantata dasu?Inaso mutane susani aduk inda maraya yakasance kar ayi wasa wajen bashi tarbiyyantar dashi da kuma karatu domin yin hakan yakansa yazamo mai muhimmanci acikin al'umma sannan kuma banzatar dashi da wulakantashi yakan iya sawa yazamo bala'i dakuma fitina acikin Al'umma.Ni atunani na wannan tarzomar Allah ne ya jarabci mutanen wannan gari bisa munanan ayyukan dasuke aikatawa sai dai muce Allah yasa mudace daga bisani kotu tana kira da kungiyoyi dake kare hakkin bil-adam dakuma nakare Hakkin yara yakama suka sance suna aikinsu bisa gaskiya dakuma yin bicike haka zalika idan kuma kunyi wannan toh fa zaku yi nasara aduk abinda kuka saka shi gaba.Sannan alkali yadanyi shiru daga bisani yaciga dacewa matasa marasa aikinyi kusan dukkan matsalanmu ya ta allaka ne bisa rashin samun shugabanni nagari. muddin Allah yakaddara maka zama shugaba toh fa kasani yawajaba kayi adalci tilas ne muyiwa matasan garin adalci tahanyar nema musu aikinyi hakan shine abinda zai taimakesu bawai mu zuba idanu muna ganin 'ya 'yanmu suna lalacewa ba,sannan kuma ina kara jan hankalin al'umma bisa daukar doka ahannu akwai kotu sabida haka duk abinda akayima kakai wajen hukuma ko kuma kashigar da wannan abin kotu.Kamar dai yadda aka kama masu laifi wadannan lafin dasukayi itace daukan hukunci dakansu gashi bisa nan daya daga cikinsu yarasa ransa, abu mafi dacewa suyi alokacin dasuka kai munzalin kwace hakkinsu shine su shigar da kara kotu ta kwace musu hakkinsu amma sai suka ki bin wannan hanyar suka biyewa son zuciyarsu tahanyar da bata daceba sabida haka wannan kotu mai adalci zataci taransu kowanne naira dubu dari da hamsin daga bisani zasuyi zaman gidan yari na watanni shida bisa laifin dasuka aikata,sannan shikuma wanda yatada tarzoma danufin martani ga wadanda aka zalunta kotu ta yanke masa hukuncin shekara guda agidan yari .Yana gefe malam Audu yace aikin banza kenan.Alkali yaciga ba dacewa shikuma maigari kotu tana umartansa dayayi gaggawan maida wannan gidan zuwa gidan marayu ma'ana agyara wajen amaidashi yanda yake sannan kuma kotu tana kiraga kungiyar Efcc dasuyi bincike akan shugaban karamar hukuma chairman sannan sukamashi bisa dukkan abinda aka samu ya tauye nadaga dukiyar talakawa.Sannnan kotu tana kira ga kungiyar kare hakkin yara ta Unicef dama duk wasu kungiyar kare hakkin dan Adam dasu kawo dauki sannan su dauki mataki bisa abinda maigari ya aikata ma wadannan marayun ma'ana su shigar da kara daga bisani kotu tayi hukunci bisa adalci da wannan muka kawo karshen wannan shari'ar.Alokacin wani yabude kofa yashigo da karfi bisa dukkan alamu daya daga cikin wadanda suka fita da maigari ne yashi go cikin kotun yana fadin Allah yayiwa mai gari rasuwa kowa idanunsa bisa kansa wane mai gari kenan chairman yatashi yatsaya alkali yadoka guduma sannan yace malam yazaka shigo kotu haka suddan,mutumin yakoma gefe yana kuka yana magana alkali yarufe shari'ar da addu'a sannan yatashi dukkannin mutanen kotun suka tashi sannan suka fara watsewa wasu suka nufi kan wannan mutumin dayashigo da labarin mutuwar maigari.Kwarai kuwa yace suna isowa asibiti Allah yayiwa maigari cikawa.Chairman yabirkice domin kuwa kusan kaso 80% na cikin dukiyar da yasata agwamnatance tana wajen maigari.Kamar zaiyi hauka yanufi gidan maigari mutanen kotu suka watse bayan ankai su Rilwan gidan yari anshiga dasu daga bisani akazo aka kirasu koda sukazo sai suka tarar da mutanensu wato Aisha da khairat da mahaifiyar Khairat dakuma Alhaji haruna da lauwali maishago da kuma kanal Idris mai ritaya yayinda kanal yake cewa shifa zai daukaka kara zuwa kotun gaba domin kuwa aganinsa awannan shari'ar ba'ayi adalciba Alhaji Haruna suka bashi hakuri barista Sani yace duka duka watanni shida ai bawani lokaci mai tsawo bane.Kawai abinda za'ayi shine hakuri akwana atashi zasu fito nan bada dadewa ba.Kanal idriss wani kallon dayake musu tamkar ya hadiyesu haka yakeji.Cikin zumudi yace ina alfahari daku tamkar yadda nake alfahari da 'ya'ya na naciki na.Zan kasance mai ziyara zuwa gareku a kowace karshen mako,sannan kuma ina maiyi muku tallar soja idan akwai wanda yakeson tafiya soja acikinku sai yasanar dani zanyi masa hanya.Sagir yace ranka dade inaso idan da hali zanje soja Aisha takallesa sannan ta tun tsire dadariya idan katafi soja wazai Aura maka zainab din?Suka kuma tuntsirewa da dariya Sani yace angaya miki sojoji basa Aurene ai sunayi idan kikaje barikin sojoji zaki samu matayensu acan.Kanal yace ka kadaine zakaje Rilwan fa?Sai Rilwan yadanyi murmushi sannan yakuma sauke kansa Alhaji haruna yace Rilwan kam inaga Shi Aure zaiyi bazashi soja ba. Suka tuntsire dadariya Rilwan yace nifa bazanyi Aure ba Alhaji inaga saidai namutu banida mata.Hajiya tace haba Rilwan menene dalilinka nafadan hakan .Rilwan yadanyi ajiyar zuci sannan yace bani ne zan bada wannan shedar ba kutambayi Sagir,kafin suyi masa magana yafara dacewa tunda aka kamamu Rilwan yake wannan furucin har abada bazai kara kula wata 'ya mace ba.Domin kuwa ataraba mace ce silar fara tabarbarewarsa yayinda tasa aka kwace computer dinsa,sannan kuma mace ce tahaddasa aka kamamu wacce tayimasa yaudara wanda bazai ta6a mantawa da ita ba har abada.Alhaji Haruna yadanyi ajiyar zuci sannan yace ai idan wannan ne kadanne daga cikin sharrin mata,amma karka kuskura ka kara cewa bazakayi aure ba.Rilwan yace toh Alhaji ni ayanzu babu wata 'ya mace da nake kaunarta wacce nakesonta kuma harga Allah ni bana tunanin akwai wata wacce zata samu gurbin zama araina ni bazanyi Aureba garama intafi soja akan nayi aure.Alhaji yace Karka damu kamar dai yadda nasamu labari Khairat takasance tana soyayya da Awwal marigayi mezai hana ka maye gurbin Awwal awajenta ma'ana zan mallaka maka ita amatsayin matarka.Rilwan zaiyi magana Alhaji Haruna yace nabaka ita Amana banaso kafurtamin wani zance kawai ka amsa ka amince ko yanzu koma yaushene nidai fatana kakulamin da ita.Shiru yayi yana sauraro yayinda Sagir da dukkan mutanen dake cikin dakin suke murmushi alokacin shikuma hawaye suke zubo masa itako Khairat kunya yarufeta gakuma abin yazomata batareda zuciyarta ta shirya ba.Alhaji yace Nizan tafi yajuya yakama Hanya hajiya takariso inda Rilwan yake tana murmushi tace wannan hawayen murna kakeyi ne ? Toh nima bari nafada maka wannan zancen nabaka ita amana kakulamin da wannan 'yar dukkan mutanen wajen sun dauka cewa kukan dadi yakeyi basusan wannan zancen da suke furtawa ta tuno masa dazancen mahaifiyar Zeenat inda take cewa karikemin wannan yarinyar nabaka ita amana kakulamin da ita wannan amanace nabaka ita.Gabadaya tunaninsa yakoma kan mahaifiyar zeenat shin awane hali mahaifiyar zeenat take ciki?Shin zeenat zata goma gida kuwa?Shin dawane idanu zai kalli mahaifiyar zeenat idan suka hadu koda alahira ne?Tabbas akwai matsala ina fatan dai zeenat takoma gida idan ko bahaka ba duk lokacin dana fito idan nacikaro da zeenat saina maida ita wajen mahaifiyarta koda kuwa dakarfin tuwo ne.Sani yakatse masa tunaninsa dacewa nima nabaka ita amana kamar yanda kabani kanwarka amana ina fatan zaka kasance mai riko da amanar da aka baka?Rilwan yadanyi shiru sannan yayi ajiyar zuci tareda gyada kai Aisha tazo tace yaya Rilwan ina tayaka murnan samun mace tagari kamar khairat yadubi Aisha tareda yin murmushi sannan yace mata nagode tajuya itama tabi su Hajiya dasuka fice acikin wajen da aka tanadar domin tattauna wa tsakanin 'yan prison da 'yan uwansu.Yarage Saura lauwali da kanal idris dakuma Sani.Sai yaciro waya yace yawwa ga wayarka nan inji ispekta Sa'ad aduk lokacin daya kunna sai kira yashigo idan yadauka kuma saiyaji wata matace take tambayarka shine yace nakawo ma Rilwan yakar6i wayar Sannan yakunna Sani yace mudan zauna mujira zakaji kira yashigo.Kanal yace musu shizai tafi amma zai dawo kowanne mako yana dubasu.Sukayimasa godiya Sannan yafita yatafi.Lawwali maishago ma yace zai tafi Sannan yayima Rilwan murna Rilwan sukayitayima Lawwali godiya sanna yakama hanya yatafi.Yarage saura barista Sani ne kadai sai su Rilwan da Uzairu ,Sagir da kuma Netmaye.Suna zaune sai kira yashigo wayar Rilwan yaduba yaga bakon lamba yadauka tareda karawa akunnensa yayi Sallama sai yaji ta amsa tafara magana maman zeenat ce.Rilwan yaji tamkar andoka masa guduma akai tafara magana dacewa zeenat tadawo ita kadai daga bisani tasanar dani dukkan abinda ta aikata maka.Rilwan yayi ajiyar zuci sannan yace kiyi hakuri maman zeenat na dauka miki alkawari kuma nakasa cikawa sannan kuma kin bani amana nakasa rikewa.Tadanyi ajiyar zuci sannan tace banta6ayin nadamar haifuwa ba sai akan wannan yarinyar yayinda tadawo da ciki sannan kuma tasanar dani irin yadda taci amanarka wai dama asali aikin kwangila takar6a akanka,Rilwan yayi ajiyar zuci sannan yace hakane mama nima nayi mamaki abinda zeenat tayimin banta6a tunanin haka zai faru ba dakuma hakan yafaru sainace Allah yasa hakanne mafi alheri,tace kwarai ma kuwa yanzu gashi shi wancan Saurayin nata shima ya banzatar da ita yanzu haka batun danakeyima bata san inda yashiga ba wai sadauki shima basonta yake tsakani da Allah ba.Rilwan yadanyi ajiyar zuci sannan yace toh mama sai ayi mata addu'a nikam yanzu haka ma ina gidan yari shiyasa kiketa kiran wayata bakya Samu,tace Allah sarki toh Allah yafitar dakai lafiya Sannan kuma dan Allah ina rokonka kayafema zeenat bisa wannan yaudarar datayi maka.Rilwan yadanyi ajiyar zuci sannan yace mama koba komaiba zan yafewa zeenat domin kuwa da yafiya da afuwa nakai matakin danake yanzu balle ma ace ke dakanki kika roka mata gafara idan har ban yafeta ba toh tabbas nakasance ta6a66e sabida haka nayafe mata harga Allah kuma har abada tace nagode Rilwan Allah yayi maka albarka yace ameen sannan takatse kiran su Sani suka zuba masa idanu wacece wannan kuma Sani yatambaya,yace mahaifiyar wannan yarinyar zeenat wacce tayaudareni din nan itace takirani wai inyafema 'yar ta bisa laifin yaudarar datayimin Sani yadanyi ajiyar zuci sannan yakar6i wayar daga bisani yace toh nima zantafi sai anjima. zanzo inke dubaku Rilwan yace nagode sosai.Yawaiga yakalli su Uzairu sannan yace idan mun fito fa zaku iya cewa zaku koma taraba fa ko?Uzairu yace hakane zamu koma sabida duk arzikinmu suna can amma nikam bazan koma harkan yahoo ba Rilwan yadanyi murmushi sannan yadubi Netmaye kaifa?Kwarai kuwa nidaga yau ma nakashe wannan sunan Netmaye sunana mubarak.Suka kama dariya Sannan yadubi Sagir wai kai yanzu soja zaka tafi?Yace kwarai ma kuwa soja zan tafi tunda akwai hanya ,Rilwan yace kaga nikuma sai in bude cyber cafe agarin nan kawai nafara sana'ata Allah yajikan Awwal da ace yana nan yau wanne irin sana'a zaiyi Allah masani sagir yadanyi shiru Sannan yadubi Rilwan yace wai me kake cikine?Shin kanason khairat ne ko kuwa bakasonta?Rilwan yadubesa kai nifa banason matsala kabi kadameni,sagir yace kaida bakinka kace mana harka mutu bazakayi aure ba ,sannan harka mutu bazaka kara soyayya ba.Rilwan yadoka masa harara kai wato haryanzu baka ta6a lura da wani abu ba, bakasan khairat ita dabance acikin mata ba? Hmmmmm ai ya wajabta na amince da ita ne shiyasa kuma itama bazan bari mudauki dogon lokaci muna soyayya batareda munyi aure ba kagane sabida tsaro....Sagir yatuntsire dadariya sannan yace nikam zamu dade muna soyayya da zainab dina kafin adaura mana Aure.Haka suka cinye watanni shida a prison sannan suka fito Rilwan suka sasanta da khairat sannan Rilwan yaje duk majalisar matasan dayake samu kusan fiye da rabi basanan sun kama sana'arsu kamfanin modern Tech kuma angyarata an mayarda ita gidan marayu andaura sabon maigari wanda yakasance mai adalci bakamar wancan ba shiko chairman tuni hukumar Efcc tanadesa shima antsigesa daga kujerar chairman din an baiwa mataimakinsa yayinda su bilal suka gama primary Aisha tagama senior set aharta huta itako Khairat tahada diploma dinta Sagir yatafi soja uzairu da Net maye suka koma taraba suka kafa kasuwanci shiko Rilwan yazama kwararre wajen sarrafa na-ura yayinda yakasance mai cyber cafe a garin...Awannan lokacin aka daura ma kowanne aure Sagir da zainab Sani da Aisha saikuma Rilwan da Khairat kanal idris shine mutumin daya dauki nauyin Auren sannan yaroki alfarmar idan fatima ta girma akwai yaronsa dayake makaranta a cairo idan yakarisa yagama lokacin tagirma yana so ya hada zuri'a dasu tayanda bazai manta dasu ba.Aka amince dazancen tahanyar yarjejeniya tsakanin lauwali mai shago dakuma Alhaji Haruna dakuma su Rilwan,,,haka suka kasance cikin rayuwa mai dadi da farinciki HAKAN TAKE...alhamdulillahi adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *