Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Thursday, April 13, 2017

KURSUM complete

adsense here

Kursum 1 to 20 Posted by XARAH ABUBAKAR on NOVEMBER 13, 2016 KURSUM by ~Xarah Bukar Page ~ Sauko wanshi kenan daga jirgin sama,daka ganshi kaga dan hutu ne,dago ne fari kakkyawan gaske,ga dara daran sexy eyes dinshi……….driver yaxo airport ya dauke shi sai cikin garin bauchi,har hotel din daya sauka driver ya kaishi…. Bayan awanni kalilan harya shirya cikin kanana kaya masu kara fito da ainuhin kyawun shi,ya kira abokinshi huzaifa dan ya yadan zaga dashi yaga gari, sun gama zagawa suka biya wani eatery dan cin abinci…… Tafe suke suna dan hira,kursum na cewa kawarta itafah ta gaji da wannan wahala su kenan kullum yan Aike suka zama, sauran dalibai na hostel amma su suna nan suna supervising kayan abincin makaranta har sai an shigar da komai kitchen,Sumy tace haba kursum miye aciki toh ai aikin lada ne kuma koba komai ai mun ga gari…………..kursum taja tsaki tace to ai sai kije ke kadai saboda ni xan dan leka gurin masu wasa da monkeys (biri). Sumy tayi kwafa ta wuce abunta inda sabo ai ta saba da halin aminiyarta…….. Kursum kenan,yarinyar yar kimani shekara sha bakwai a duniya,ga kyau, sam batason hayaniya, amma idan ka tabo ta sai inda karfin ta ya kare Wannan kenan…. *Xarah Bukar* *Dedicated to Bady social* ~Luv u all~ KURSUM By ~Xarah Bukar Page ~ Gaskia garin nan fah akwai mata hadaddu, ya kamata ace kafin in bar garin nasamu babe (yarinya) wanda xan huta da ita, huzaifa yaja tsaki ya kalle shi kaidai yazid kana nan da halinka na playing mata bansan randa zaka natsu ba, Ina fatan Allah yakawo wacce za tayi maganin ka……….Yazid yace aini babu macen data isa tayi magani na, asali ma ban dauki su abakin komai ba face rigar canxa wa Sumy ta gama aikin da take ta biya eatery cin abinci, shiganta kenan tayi ido hudu dashi, wow ta fada cikin xuciyan ta gaskia kiya guy dinnan is hot ya hadu iya haduwa…. bata ida xancen xuci ba kawai taji ya mata sallama ai ba shiri ta saita kanta ta amsa ta gaishe shi, da fara’arsa yace mata ni sunana habib acewar yazid Ina fatan baza kimin rowar sunanki ba… tayi murmushi tace sumayya suna na yace nice name sumy Ina kike xama ne naganki da school uniform, tace aikina director dinmu yayi school din bayan wajen nan yake ma, yace okay nagane skull din. Yayi murmushin mugunta yace naga kinmin ne gashi you are so quite Ina fatan dai xaki amsa min tayina, sumy ta sunne kai xuciyan ta fal da farin ciki, yau dai ta samu prince charming din da take mafarki…….. yazid ya dauko wani hadadden xoben azurfa mai shegen kyau da tsada ya zurawa mata a hannunta amatsayin son dayake mata sumy tayi godiya tace zata wuce dare ya farayi yace yaushe xamu sake haduwa, tace ko xuwa gobe muna iya haduwa anan yace toh Allah kaimu ta wuce. ……. yayi murmushi mugunta da alaman yarinyan bata da wayo, tabbas zan samu abunda nake sha”awa tattare da ita..ya wuce waje wajan abokin kinshi daya cika yayi fam dan jiran ya dawo su wuce huzaifa yace Allah ya shirye ka yace Amin suka wuce……. Ina Kursum take ne? Waye yazid ? Wace kuma sumy ? Mai yakai kursum da sumy makarantar boarding wanda babu marabarta da gidan marayu ? Ku buyoni dan jin asalin labarin *Xarah Bêê* *Dedicated to Bady social* ~Luv u all~ KURSUM By ~Xarah Bukar Page ~ Har kusan yamma sannan ta dawo, ta tadda sumy kwance sai faman murmushi take tana lumshe idon ta kursum ta daka mata duka tace lafiya ki kike wani murmushi kaman wata charisma goat (akuyar krisimeti) ko dai baba ne ya shigo gari, sumy tace kedai yau nayi new catch fah guy din ya hadu iya haduwa ba karya, wani irin so da kaunan shi ke ratsamin zuciya……….. Kursum ta yatsane fuska taja tsaki, kedai raba kanki da soyayya tun yanxu saboda maza basu da tabbas kila ma dan iska ne, sumy tace haba banda habib dina dan kuwa nasan yana sona, munyi dashi ma xamu hadu gobe dan Allah kursum ki taimaka ki rakani gobe kinji my cwt sis:| Yazid kwance a tafkeken dakin hotel din daya sauka da alama waya yake, yace haba xee kiyi hakuri mana nace makin nan na 4days xan dawo duk kin dakamin hankali….xee tace haba ya yazid tun jiya fa yakamata ace ka dawo wlh nayi missing dinka sosai gaba daya garin kano yamin zafi, jiya har wajen ummanka naje na mata wuni ko zan kanga amma shiru kuma gashi wayoyin ka duka akashe…..kiyi hakuri my love zan dawo dana gama aikin dana ke abubuwa sun min yawa ne, tace to amma dai kayi promising nan da 4days ko yace eh ya kashe wayan……xee rigiman ki yayi yawa wlh amma dole in koma saboda dad bai san bana gida ba. Makaranta ce babba nagani nafada mai tsadar gaske wanda sai dan wane da wane, ita ba gidan marayuwa ba kuma bawai makaranta jeka ka dawo bane ko boarding, yawan ci student (dalibai) din dake makarantar iyayensu basu da lokacin kula dasu, tun yara na kanana ake kai su har sai sun gama senior year sunkai 18 years old (shekaru goma sha takwas) Sannan iyayen su ke zuwa daukan su…….Gimbiya Hafsatu itace director din makarantar gata da zalama dason abun duniya,babu ruwanta idan kakai 18years iyayenka basu zo daukan kaba saita aurar dake acewarta iyayenka sun manta dakai ne…… Yau ta kama weekend fito wansu kenan daga hostel zasu shiga gari, daka gansu kaga aminan juna ….kursum tace kin tabbata saurayin nan naki zai zo, ina fatan dai ba jirga ki zai yiba sumy tayi dariya tace haba dai aini na yadda dashi dari bisa dari, maybe ma yana can yana jirana ma Sun iso wajen haduwan kenan sumy tace wayyo na manta da xoban daya bani jiya akan gado kuma gashi namai alkawarin bazan cire shi ba dan Allah kursum kiyi hakuri ki jirani anan barin koma hostel in dauko. Kursum ta wurga mata harara, tace kedai wallahi baki da wayo sam, dan wahala shine xaki koma ki dauko toh ai sai kije ni ina nan idan kuma kin dade in kara gaba abuna, “sumy tayi murmushi ta bar wajen da sauri ta. Tana nan tsaye har kusan minti goma, taji wani lausassan murya yana mata sallama ta juyo sukai 4 eyes saida numfashin ta ya kusa dauke wa saboda ya hadu iya haduwa, ya sakan mata wani irin yaudararen murmushi, ta hade rai tace malam nasan kane, yazid yace a’a baki sanni ba, asalima ni bako ne yau Nashigo garin suna na kabir yana murmushi yana shirin jawota jikin shi, ai bai ankara ba ta wanke shi da mari an gayama ni yar iska ce, waye ma kai dahar xaka naimi tabani………kallon ta kawai yake yana shirin magana sumy ta iso wajen fuska a murtuke tana tambaya meke faruwa taja kursum gefe tace shine saurayin nawa fa naga kina shirin yimai rashin mutunci kursum tace sis ki raba kanki da guy dinnan kabir ban yadda dashi ba da alama yana da wani hidden agenda tattare dashi. Sumy ta daure fuska tana mata kallon bakida hankali wato bakin ciki kike min danke baki da saurayi toh baki isa ki rabani dashi ba yanxu nafara sonshi kuma harda aure xamuyi, sunan shi habib not kabir tayi tsaki ta bar kursum nan tsaye da mamaki. Yazid yace amma kawarki bata da mutunci tana ganina tafara zagina, sumy tace dan Allah kayi hakuri kar kayi fushi bata sanka bane, yace to ya wuce ya kike me zan samu ne yana magana yana rike da hannunta yana lashe lips dinsa sai lumshe ido yake, tace lafiya kalau nake” anan garin kake zama ne yace eh ai gidanmu bai da nisa daga nan, iyayena sun rasu, wajen kawuna nake tun ina karami tace wayyo Allah yaji kansu da rahma ta tausayamai sosai wani irin sonshi ke kara shiga zuciyar ta….. Ni yanxu bani da kowa sai kawuna sai kuma ke, “ya kara janyo ta jikinshi yaxe plz sumy karki kujeni I love you with all my heart, xaki aureni ? “Ba shiri sumy tace eh kaman dama jira take ( I pity u sumy) , yace to yanxu ya zaai Kince parent dinki suna kano kuma ni inaso in mallake ki amatsayin mata ta, tace babu damuwa babana sau daya yake zuwan min visting a shekara kuma yana sona sosai idan yaga na auri wanda nakeso shima zai ji dadi, yanxu kawai director din makarantar mu Gimbiya Hafsatu xaka samu sai kuyi magana saika turo a naimi auran ko gobe kakeso ana iya daurawa….. Shi kam sai kallonta yake azuciyan shi yace lailai yarinyan nan bata da wayo ko kadan, burina kawai in samu abunda nasamu in tattara in gudu bazama ta kara gani na ba. Yazid yace kina ganin babu matsala danni acikin kwana uku nakeso ayi auren dan baxan iya rayuwa bake ba, tace babu matsala gimbiya Hafsatu tasan abunda ya kamata…ya rakota har gaban makarantar sannan sukayi sallama ta wuce ciki shima ya tafi yana farin cikin da baisan na miye ba. Hmmmm Muje xuwa dan jin cigaban labarin *Xarah Bêê* *Dedicated to Bady social* ~Luv u all~ KURSUM By ~Xarah Bukar Page ~ Tangareren Mansion (gida) ne mai girman gaske kaman estate, da ganin gidan kasan dukiya ta zaunawa masu shi……. Hajiya hadiza ce zaune acikin kataferen parlour din gidan wanda yasha dukiyar gaske da kayan alatu…. Fuskan nan nata ba annuri :evil::evil::evil: ko kadan, tasha uban shade (tabarau) a ido….taja dauri har goshi irin no respect dinnan, tana jiran sauko wa Alhaji Tanimu danta zazzaga mai masifar data saba. Alhaji ya sauko yana wlh hadiza baki isa ki hanani xuwa ganin yarinyan nan ba kuma dole in dawo da ita nan da xama tunda gidan ubanta ne, haba wai yaushe xaki canza halin ki ne tunda na aurenki bance Alhamdulillahi ba saboda bakin cikin da kike shuka min. Ta ja tsaki tace indai ka dawo da sumy gidan nan toh saidai nafita in bar maku gidan, kawai dan ya’ta ta rasu shine ka samo yarinya a titi ka kawo gida kana rainonta shekara da shekaru, gaskia Alhaji ka canxa Shawara. …:evil::evil::evil: Alhaji yayi kwafa ya fice daga gidan, yana mamakin halin rashin imani irin na hadiza, “duk da ta makance, amma babu halinta daya canxa. Alhaji tanimu da malam habu (baban hajiya hadiza kenan) aminan juna ne sosai, kafin malam ya rasu ya roki Alhaji ya auri hadiza tunda bai sake aure ba tun bayan mutuwar matar shi ta farko, yace hadiza ta manya ta ga shekaru sun ja amma shiru babu manai ma….dalilin auren alhaji da hadiza kenan. Hadiza ta tsani alhaji sosai, ita aganinta ta wuce ajin da zata auri tsoho kusan sa”an ubanta..koda tayi rashin yarta wajen haihuwa bata damu ba, amma sai ta nunawa alhaji ta damu sosai har a sanadiyar haka tasamu ciwon ido ta makance Wacece kursum ? Kursum marainiyar Allah ce bata da kowa sai sumy , ranar da uwarta ta haife ta tayi niyyan jefar da ita atiti tare da ajiye mata 17 white diamonds (lu’u lu”u) da pink daimond guda daya tare da rubuta kursum ajikin wani hankecheif pink mai kyau amatsayin sunan data ba yarta acewarta duk wanda ya tsince ta bazaiyi wahalan rainonta ba tunda ga dukiya……….amma aminiyar uwarta mairo ta tausayawa jaririyar ta bada shawaran kaita inda xaa raineta harta girma, shine mairo ta kaita makarantar da take yanxu ta damka ta hannun gimbiya hafsatu sannan tabata 18 diamonds din acewarta duk shekara adauki diamond daya a biya mata kudin makaranta da abubuwan da zata bukata, sannan idan yarinya ta cika shekara goma sha takwas sai abata pink diamond din dan tasamu na rike kanta a rayuwa. Wacece sumy ? Sumy diyace ga Alhaji tanimu da hajiya hadiza, asali yan kano ne, tun tana karama alhaji yaje gidan marayu yayi adopting dinta arashin rasa yarsa da yayi tun haihuwan ta, shiyasa ya dauki son duniya ya dorawa sumy, sabanin hajiya hadiza data tsane ta kaman mutuwan ta……dalilin da yasa ma alhaji ya dauke ta tun tana shekara hudu a duniya ya kaita makarantar da take yanxu haka, wajen shekara goma sha uku kenan hajiya bata sata a ido ba Wanene Yazid ? Yazid Imam Ambrusa, dan kimanin shekara 29 a duniya, “da tilo ne ga alhaji imam da hajiya mairo, cikakken haifefen dan kano ne, abunda yaga dama yakeyi iyayensa basu wani damu dasa masa ido ba shiyasa bai dauki mutane da relationships abakin komai ba…….. huzaifa ne kadai abokin shi tare suka yi school of aviation dake kasar England, yanxu haka shi yazid din cikakken pilot (matukin jirgin sama) ne, shine manajan company din babansa na jirgin sama….Ambrusa & Sons Airline. Wacece xee Zainab diya ce ga baba shehu (kanin hajiya hadiza)…..mamanta ta rasu tun tana karama, shiyasa ita da baba shehu suka dawo Mansion din alhaji tanimu da zama….zee irin yammatan nan ne mara sa kamun kai da aji duk girman mutum haka zata kalle shi ta shuka mai rashin M,”ga ubanta da shegen son abun duniya burin shi kawai alhaji ya mutu suci gado.. Babu wanda take so a duniya kaman yazid Ambrusa, asalima ita ta makale mai harya fara bata attention…..babu wanda bai sansu tare ba, burinta kawai ta aureshi yaxama nata. *cigaban labarin* Kursum da takaici ya isheta haka taja jikinta ta dawo hostel tayi kwanciyan ta, gaba daya duniyan tai mata zafi wato akan saurayi shine sumy zata ci mata mutunci hmmmm……amma fa guy din ya hadu ba karya, fuskan shi kawai take gani, wani irin nishadi take shi, “taja tsaki Allah ya rabani da irin shi dagani ma dan iska ne, tunda naga alama suna biyu gareshi. Turowan kofan dakin ne ya dawo da ita daga tunanin da take, sumy ce ta shigo ko kallon gefen kursum batai ba……haka dai suka kwana suka tashi babu wanda ya cewa wani uffan. Gimbiya hafsatu taga kudi sai washe baki take, tace indai sumy ce nabawa danka halak malak, kawu jamilu (wanda yazid yayi hayan sa ya bashi makudan kudi yaxo amatsayin kawun sa ya naima mai auren sumy) sai zuba godiya yake kaman dagaske, yace yaron nawa fa yafiso adaura auran nan da kwana biyu……gimbiya hafsatu tace ai angama, ya mika mata dubu ashirin amatsayin sadaki ta amsa tana Dariya. Hmmmmm *Xarah Bêê* *Dedicated to Bady social* ~Luv u all~ kursum 21 to 35 Posted by XARAH ABUBAKAR on NOVEMBER 13, 2016 KURSUM By ~Xarah Bukar Page ~ Haba sumy yanzu da bakinki kika aminci da auran stranger din da baki ma san halinsa ba, ko aure baki sani ba balle iya zama da miji asalima ma ko dadewa bakuyi da haduwa ba…… Dan Allah kursum ki kwantar da hankalinki kema kinsan banda wani option daya wuce in aure shi tunda har muna son junan mu, kuma nidai akan in koma gurin momy da zama na gwamma ce in auri stranger dinnan cause hankalina yafi kwanciya dashi I don’t want to lose wannan opportunity din dana samu, kursum tace to mai zaki cewa daddy kinsan nan da wata biyu zaizo ganinki, tace dad ba matsala bane, na tabbata sai yafi kowa murna da auran nan. Kursum tace toh Allah yasa hakan yafi alkhairi, duk jikinta yayi sanyi ranta abace ta rasa dalili,:|:|:| tana ganin dan zata rabu da aminiyar ne shine yasa ta jin hakan. **************************** A yau ne aka shaida daurin auran yazid (habib) da sumy, babu wani event da akayi illa abinci da gimbaya hafsatu ta bada a dafa, anci an koshi jama’a sun watse kafin dare kuma akai amarya Ango kam sai washe baki yake, :mrgreen::mrgreen::mrgreen: babu wani aboki ko dan’uwa dayasan da batun auran face kawu jamilu daya tsaya mai akai komai cikin kwanciya hankali… Ko huzaifa abokinshi bai san abunda. Ke faruwa ba, dan yasan idan ya gayamai plans dinshi xai ruguje kenan, asalima yamai karyan ya koma kano. Amarya sumy sai shiri take tana hada kayanta cikin akwati, farin ciki fal fuskan ta, lokaci kawai take jira akaita gurin heart beat dinta. Ta kalli kursum data takure karshen gado, daka ganta kasan tana cikin tashin hankali….tace haba sis muna nan tare fa bawai guduwa xanyi in bar kiba, kursum tace dole hankalina ya tashi bani da kowa sai ke sumy, idan kin tafi maraicina zai dawo sabo ta fashe da kuka mai tsuma zuciya, sumy ma tana kuka tazo ta rugumeta tana kara bata baki akan tayi hakuri suna nan tare, mutuwa ce kadai xata iya raba su. Da daddare kawu jamilu da kanshi yazo dauka amarya, gimbiya hafsatu da kursum kadai suka mata rakiya har gidan mijinta, Gida ne dan karami, mai dauke da room & parlour sai kitchen daga gefe sai dan karamin tsakar gida, cikin dakin kuwa babu wani abun kirki aciki sai kafifa kawai da stool na zama, dama baa jera mata komai ba tana jiran idan daddy ya zo sai ya siya mata komai da komai. Gimbiya hafsatu da kursum sun mata nasiha sosai, sanna suka mata saida safe suka wuce abunsu. Kamshin turaren sane yasa tagane yashigo dakin, yaxo ya xauna kusa da ita ya jawo hannuta ya sumbata yana kare mata kallo, yarinyar so innocent………. Sakonnin soyayya ya aika mata a darenan da kyau,masu rikitarwa, har ya samu biyan bukatan shi, saida yaji kukanta na yawa sanan ya dan saurara mata…… Koda ta farka da safe baya cikin dakin, dakyar ta tashi ta shiga toilet ta tsarkake kanta tayi wanka ta fito tayi sallah harta koma bacci, sai wajen 10am ta tashi, tayi mamanki still baya na,ta tashi ta leka ko ina a gidan amma bayanan kuma babu alamunsa…… Ta koma daki dan duba kayan sa, nan ma wayam tagani sai wata wasika daya ajiye mata kamar haka Matata mai sona, Allah yayi miki albarka kin biyani ni arayuwa…….amma dan Allah ina naiman gafararki da ki yafemin dan bawai na aureki dan ina sonki bane face sha’awarki danayi, kuma ni bazan iya zina ba shiyasa na aureki, amma kiyi hakuri sumy, na sakeki saki biyu sannan ga kudade masu yawa nabar miki ki kula da kanki, karma kice xaki naime ni dan kuwa baxa ki taba ganina ba. Sannan kina iya zama acikin gidan na wata daya kafin kudin hayan ya kare…………..ina miki fatan alheri. Bissalam Innalillahi wa inna’ilaihi rajun kawai take fadi, ta fadi kasa tana rusa uban kuka shi kenan taga ta kanta kursum ce ta shigo gidan da abincin karin su, ba karamin girgiza tayi ba da taga kawarta cikin yanayin nan tace miya faru? Kukan mai kike yi? baki da lafiya ne, a gigice take jero mata tambayo yi……… sumy kam kasa cewa komai tayi, ta mika mata wasikar daya ajiye mata, kursum ta girgiza matuka data karanta kasa cewa komai tayi, itama ta zauna sai kukan suke babu mai rarrashin wani. kaico Daga bisani suka tashi suka dau kayan sumy da makudan kudin daya bari suka bar gidan….. Yazid kuwa tunda ya tashi yawuce Airport yana sauri baya son missing flight dinshi na 7am, Allah yasa yana xuwa dama shi kawai ake jira, jirgi ya daka sai kanon dabo……. Umma ce da kanta taje dauko shi a airport, dan kawai yasan ta damu dashi, suna cikin mota umma tace, son wato ka gujemu ko, wajan wata daya kenan bansa ka a ido ba idan nakira wayan ka saika ga daman dauka…… Yace to umma ya kikeso inyi, keda kika fi bawa aikin ki (fashion designer ce) mahimmanci, ko a gida baki da lokacin kowa saina aikin ki, ki wuni kina aiki a office kuma ki dawo gida kinayi, har Abba ma yafiki samun lokaci na, “tace my son kamin uzuri dan Allah, aikin nawa ne dole saida attention sosai in ba haka ba komai bazai yi daidai ba, ni kaina inason kasance wa da family dina shiyasa ma nakeson daukan hutu kona wata biyu ne……yace toh shikenan umma duk yadda kikai yayi daidai, shidai arayuwan shi yanason ummansa bai hadata da komai. Koda gimbiya hafsatu ta karanta wasikar sumy, sai cewa tayi karta damu dama maza basu da tabbas, itama tayi mamaki yadda yayi ta zubar da kudi kaman bai san ciwon suba, indai aure takeso zata iya naima mata wani ta aura kodan ta huce haushi. Kursum tace haba gimbiya kamata ace kin naimo mijin nata ayi magana,tunda da hadin bakinki akayi auren nan kuma ai kinsan kawunsa, gimbiya tace tab aini yanxu ko nayi trying number kawun bai shiga kashe wayar take kuma yarinyan ita da kanta ta nuna shi take so kuma xata aure shi, toh miye laifina aciki…….ki fice min yanxu nan marar kunya, wato kece da bakin magana ita da aka saka bata zoba sai ke, wawiyar banza. Kursum ta fice ranta abace,bata taba ganin zalamar miyar mata irin gimbiya ba, ita dai kanta kawai tasani…… Ta koma dakinsu, har lokacin sumy kuka take duk ta rame ta fita hayyacinta lokaci daya, kursum tace mata dan Allah ki bar kukan nan haka, indai ina raye a duniya toh saina naimo shi na daukar miki fansar abunda ya miki, koda kuwa zaiyi causing life dina, dat is a promise, sau daya nataba ganinshi amma bazan taba mantawa da face dinshi ba…… Tana taba sumy baki hardai ta hakura ta barwa Allah komai.. *Bayan wata biyu* Sumy sai rashin lafiya take ga zazzabi da weakness da take ji ga yawan amai , shiyasa gimbiya ta kaita asibiti, doctor ya mata gwaje gwaje ya gano tana dauke da cikin wata biyu…….aka sallamo su suka dawo. Gimbiya ta kirawo kursum ta gayamata sumy na dauke da cikin wata biyu, sai data girgiza da jin wannan xancen, yanxu ya sumy zatayi idan tasan tana dauke da cikin wanda yama manta da zamanta, gimbiya tace ga test result din saiki bata ki kara kwantar mata da hankali, kinsan mai karamin ciki batason tashin hankali gudun kar ciki ya zube. Ta karba sum – sum ta fice, tasamu sumy na karatun al-qur’ani, sai da tajira ta idar sannan ta mika mata test result din, sumy ta karba ta duba saida gabanta ya fadi tace wake dauke da ciki ? Kece kowa? Kursum tace kinsan dan Adam ajizine, duk yadda ubangiji ya tsara aka ke faruwa babu wanda ya isa yaja da ikon Allah, komai na duniyan nan jarabawa ce, Dan Allah kiyi hakuri ki yarda da kaddaran da Allah ya daura miki, sumy tace meke faruwa ne ? kinsani a duhu fah. Ciki gareki na wata biyu sumy, kece keda cikin ba kowa ba, hawaye kawai sumy take tana addu’an Allah yasa hakan yafi alheri agareta, kursum tace amin. Daddy ne ke tuki hankali kwance, yana murnan yau zai ga diyar shi tilo a duniya, wajen shekara guda rabon daya ganta.. Ya iso makaranta, har visitors lodge (inda iyaye ke zama idan sunzo ganin ya’yan su) aka kaishi, aka tura kiran sumy tazo dad dinta yaxo…..ita da kursum suka je wajen daddy suka gaishe shi, gaban dad sai da yafadi ganin yadda sumy ta rame sai haske data kara sosai, yace kursum, sumy bata da lafiya ne? Kursum tayi shiru ita dai tarasa dalilin daya sa idan tana gaban baban sumy take jin wani iri, kaman akwai wani connection tsakanin ta dashi………kukan sumy ne yadawo da ita daga tunanin da take, tana kuka tana ba daddy labarin abunda ya faru tun daga auran ta har izuwa yanxu da take dauke da ciki, daddy kasa magana yayi sai hawaye kawai, gaskia ya tausayawa sumy ba kadan ba, duk laifin hajiya hadiza ne, da yanxu sumy na gida agabanshi hankalinta kwance. Yana taba sumy hakuri akan karta damu jarabawa ce ta ubangiji, komin wuya akwai dadi, ya ajiye masu shopping din daya masu sa’annan ya masu sallama zai koma kano, karshen shekara zai dawo ya dauketa, ya dauko makudan kudi yabasu suna ta godiya.. Daddy kam yayi niyyan kwana biyu, amma bazai iya jure ganin sumy halin da take ciki ba, shi kanshi daurewa kawai yake amma ranshi a bace yake, aka ya tattara ya koma kano, Hajiya hadiza na hakimce a parlour a zaune tana jiran shigowan daddy gidan, dan ta kwarara mai buhun bala’in data saba akan yaje ganin yar tsintuwo bada izinin taba…. Yana shigowa ta gane muryanshi da sallaman da yayi bata ma damu da yanayin shi ba, ta hau zaginshi damai rashin kunya ta ko ina, daddy kam kasa magana yayi ma saboda bakin ciki ta riga tamai yawa, nan take shikam ya yanki jiki ya fadi sai jin faduwan mutum tayi tim akasa…..:oops::oops: Ta kwallawa samira (yar aiki) kira maza ta fito Alhaji ba lafiya, samira ta fito da gudunta tana hajiya, alhaji ne ya fadi da alama ma rai yayi halinsa. Hajiya a rude tace “samira kiramin wayar shehu nasan baiyi nisa ba,kirashi mukai alhaji asibiti….. Baba shehu da sauri ya iso gida,suka sa alhaji a mota sai asibiti likitoci sun yi iya kokarinsu, amma rai yayi halinsa (kulli nafsin za’ikatul mauti), abun tausayi hajiya da baba shehu sai kuka suke yau sunyi babban rashi. Doctor yasamu baba shehu da hajiya ya tambaya su ya akayi suka bari har zuciyan alhaji ya buga alhalin sunsan yana da ciwon zuciya, hajiya tayi tsuru tsuru bata ce komai ba illa kukan da take tayi dan tasan tabbas itace silan ciwon zuciyan alhaji, yanxu gashi ya tafi ya barta, kuka kawai take tana nadaman abunbuwa data shuka mai…….. Nima kasa rubutu nayi saboda mutuwan daddy ba karamin girgizani yayi ba…… Rip *Xarah Bêê* *Dedicated to Bady social* ~Luv u all~ KURSUM By ~Xarah Bukar Page ~ *Kano* Mutuwa daddy ba karamin girgiza jama’a tayi ba, mutane da dama sun sanshi da halin kwarai da taimakawa talakawa, Sam ba ha’inci ko xalinci a lamarin sa……mutane sai shigowa ta’aziya suke, baba shehu na daga waje yana amsan gaisuwa… Hajiya kuka kawai take dakyar take ma iya amsa gaisuwan da ake mata, hajiya mario ce tadawo gefen ta tana kara bata baki akan tayi hakuri addu’a ya kamata tamai bawai kuka ba. Zainab ma tayi rashin daddy ba kadan, dan daddy ne kadai yake kwabarta da mata nasiha sosai game da yanda tadau rayuwa da zafi, yau gashi tayi babban rashi. Tana kaunar shi tamkar shiya haife ta.. Har gida yazid yaje yama xee ta’aziya, ya tausaya mata sosai dan yasan yadda suka shaku da daddy ba kadan ba, wani irin sonta ya karaji a zuciyan shi….har dakin hajiya yaje ya mata gaisuwa, ta amsa ba yabo ba fallasa dan yanxu tadan rage kukan nata, dazai wuce ta bashi sako ya kaiwa mairo tare da shi mai Albarka. ……..yazid kam yana jin haushin yadda hajiya ke cewa umman sa mairo sai kace a kauye Ina laifin maryam ma…… Bauchi Yan makaranta kam sai shirye shiryen xana jarabawa shiga ajin karshe ake babu wasa kowa ya dukufa da karatu, sumy kam ciki ya shiga wata tara, haihuwa ko yau ko gobe, “Sam bata da labarin mahaifinta ya rasu wata bakwai da suka wuce. Kursum da gimbiya kadai suka San da rasu war shi, sunki sanar matane akan lalular da take tare shi. Sun fiso saita haihu sannan su gaya mata….. Bayan kwana biyu, sumy ta tashi da nakuda mai tsanani, da gudu kursum ta kira gimbiya sukai rushing dinta zuwa hospital , Allah yasa haihuwan taxo mata da sauki ta haife kakkyawan baby gal wanda babu bambamci da ubanta kaman an tsaga kara an karya…washe gari likita ya sallamo su suka dawo… Ranan suna ba wani bidiri akai ba, duk da gimbiya ta gayyato mutanan ta, yarinya kam taci suna hanifa son kowa kin wanda ya rasa. Sumy kam sai murna take, ba karamin son hanifa take ba, dan yanxu tama daina jin haushi mijinta asalima ta yafe mai duk abunda ya mata…tana fatan Allah ya hada hanifa da ubanta wata ran. Kursum ce ta shigo daki ta kwantar da hanifa da tayi bacci, tace akwai abunda nakeson gayamaki sumy amma kiyi hakuri bamu gayamaki ba tun lokacin saboda cikin ki, Allah ya yayiwa daddy rasuwa tun wata takwas da suka wuce…. Innalillahi wai inna’ilaihi raji’un kawai sumy take furtawa, kuka take na tashin hankali shikenan daddy ya tafi ya barta yanxu bata da wani gata, yanxu ya zata koma gida da zama, dan bata manta da azabar da tsanar da hajiya ke mata ba tun tana karama, hawaye kawai take tana Allah yaji kanka da rahma daddy……Kursum kam tashi tayi tabar dakin dan bazata iya ganin kawarta cikin yanayin da takeba…….itama tasan tayi rashin daddy ba kadan ba, dan shine ya mamaye mata gurbin uban da bata dashi. *kano* Gaba daya family din daddy sun hallara a parlour din gidan tare da lawyer (alkali) sa dan karanto will (wasiha) da alhaji ya bari kafin ya rasu…… Baba shehu kam sai murna yake dan yasan dole yasamu abu mai tsoka, dan tun rasuwar daddy ya maida kanshi managing director din oil company dinsa. Mommy da xee suma suna zaune suna jiran barrister yafara bayani.. Barrister shu’aibu ya fara da addu’an sannan ya fara bayani yace tun lokacin da alhaji yakamu da ciwon zuciyan yasan bazai dade ba, shiyasa yazo ya sameni ya bani takardar nan, acewarsa duk ranar da baya duniya yanaso acika masa burinsa dake rubuce anan……barrister ya Bude yafara bayani kaman haka Ni Alhaji Tanimu Bawa na damkawa ya’ta sumayya dukiyata kashi hamsin acikin kashi Dari, sannan na bata matsayin managing director na oil company dina da kuma gidan da muke ciki duk na mallaka mata su. Acikin kashi hamsin daya rage na bawa hajiya hadiza kashi ashiri, kashi goma na bawa Zainab, kashi goma na bawa shehu sai sauran kashi goma akai masallaci da gidan marayu. Ina fatan iyalaina zasu cikamin burina , sannan banyi haka danna matawa wani ko wata rai ba…..bissalam Barrister ya gama karantawa sannan ya mikawa mommy takardar, yace alhaji yamai xancen nan da shekera daya atura driver yaje ya yaje ya dauko sumy daga makaranta, mommy tace to insha Allahu xaai haka, barrister yamasu sallama yatashi ya tafi. Baba shehu kam fuskan nan babu annuri ko kadan, wato haka alhaji zai sakamai duk irin kokarin dayama company dinsa shine zai bashi 10% kawai acikin uban dukiya daya tare, kuma harda ba yar’sa director din company din, yarinya karama da komai bata sani ba, “Yayi murmushin mugunta da tunanin halaka yarinya kafin ma ta shigo gidan nan.. Hajiya kam bata damu da abunda tasamu ba asalima abun duniya bai dameta ba, takai cinta daya shine yadda alhaji ya bawa sumy komai daya mallaka alhalin bama yar’sa bace ta jini, zata bar sumy ta zauna a gidan amma tayi alkawarin making life dinta miserable. Zee sai murna take, dan batama yi expecting samun wani abu ba, tunanin ta daya shine Wacece sumy ya take, itadai tasan sumy diyar alhaji da mommy ce amma bata taba ganinta ba. *Bayan shekara daya* Sun gama exams sai shirye shiryen tafiya suke, kursum dake wasa da hanifa tace sis yanxu kina ganin idan nabi ki gidanku ba matsala , nidai ina tsoro kar hajiya tamin wulakanci ta kore ni, dan yanda kike ban labarin halinta na rashin kirki nasan tana iya wa. Sumy tace karki damu nasan yanxu ta canza tunda shekaru sun ja, kuma makauniya ce ba lailai bane tasan kina gidan ba…… An turo driver daga gida daukan su, sai sallama suke da kawayen su da sauran malaman makaranta , suka shiga har office din gimbiya hafsatu sukai mata sallama ta dauko wani dan karamin box ta bude taciro wani hadadden pink diamond da take ajiye dashi wajen shekaru goma sha takwas da suka wuce ta damka wa kursum a hannu, tace yaudai na cika alkawarin, kursum tace wanna na miye kuma, gimbiya tace matar data kowa kine tun kina jiririya tace in baki idan kin tashi tafiya kya iya siyarwa ki samu na rike kanki, Kursum tai mata godiya sosai suka fice, sun iske driver na jiran su, suka shiga mota… koda suka shigo cikin gari sun tsaya suka shiga gidan Inna sadiya (mai kitson su) suka gaishe ta sosai ta amsa da fara’arta dama tasan da zuwan su, sumy ta mika mata hanifa, Inna ta amshe ta sai wasa take mata tace karku damu zan rike muku ita har kudawo daukan ta dama nagaji da xaman kadaice. ….. Kursum tace Inna mungode sosai, da munyi settling zamu zo mu dauke ta yanxu ki rubuta mana number wayan ki yadda idan mun isa gida zamu kira, dan yanxu ba waya ahannun mu, “Suka bata kudi masu yawa wanda zai ishe su kafin su dawo, suka kama hanya sai kanon dabo… amota sumy sai kukan rabuwa take da hanifa, tabbas tasan barin hanifa wajan Inna shine daidai dan tasan hajiya bazata taba yadda da cewan tayi aure harta haihuwa ba, shiyasa ma tabar ta hannun Inna kafin tasamu yi mata bayani. …… Sun shigo kano kenan, sumy tace gaskia yaka mata kindan gyara fuskan ki kodan kwalli ne kisa a ido, kursum tace kinsan ni bana kwalliya asalima ko kayan kwalliya ban dashi, sumy ta mika mata handbag dinta tace bude kidau powder ki sha fa, Daidai lokacin da kursum ta amshi jakar sumy wata katuwar motar petur dake tafe ta bangaje motar su, kofan side din da kursum ke zauna ya Bude ta fado kan titi rike da jakar sumy, sai birgema take harta buge da wani katon dutse, sumy da driver kam suna cikin mota dake kamawa da wuta sai gangarawa motar take cikin daji harta bugu da wani katon bishiya tayi exploding baammm kawai kake ji. … :oops::oops::oops::oops: *Xarah Bêê* *Dedicated to Bady social* ~Luv u all~ KURSUM By ~Xarah Bukar Page ~ Kursum ta farka taganta a gadon asibiti, duk jikinta ya kurje ga farin bandage da aka daura mata a kai dan tsayar da jinin dake zuba, sai kuka da ihu take tana Kiran sunan sumy. Da gudu wanda ya tsince ta a hanya ya kawota asibiti yaje ya kira doctor malik yana gayamai patient din ta tashi amma kaman bata hayyacinta… Doctor ya shiga yana mata magana, amma ita kam ihu kawai take tana Kiran sumy, ya tsira mata allurar bacci ya fito. Yace Bala daka tsince ta babu waya ahannunta ko wani abu dazai sa musan family dinta ko inda take zama, Bala yace gaskia babu sai dai ko jakarta xaa duba, dan koda na ganta akwai karamar jaka tare da ita, ya mikawa doctor malik jakar, suka zazzage jakar daga kayan kwalliya sai wani wallet mai kyau suka bude, pictures din daddy kuda biyu Dana kursum ne aciki sai wani karamin littafi an rubuta sumayya tanimu bawa. Doctor malik yace ai wanan hoton alhaji ne, kuma ba shakka wanna yarinyar yar’sa ce amma to ina taje harta samu accident, ya kalli Bala yace mungode sosai da taimakon da kayi, nasan family din yarinyan kuma yanxu zan kirasu awaya suzo su dauketa, nine family doctor din su. Bala ma yamai godiya sannan ya wuce. Doctor malik ya kira mummy yamata bayanin komai, tace tabbas yar’ta ce dan dama tun wajen kwana biyu daya wuce akaje dauko ta daga makaranta, amma sukaji shiru basu iso gida ba, an duba hanya an gano motarsu tayi hatsari ta kone sai gawan mutum biyu akone kawai aka gani, kuma ance mana tare suke da kawarta daga makaranta, doctor yace kawar ce ta rasu da driver kenan, dan yanxu haka sumy na nan kuma jikinta yayi sauki sai dan ciwon da baza’a rasa ba, tayi mai godiya sosai tace zata turo baba shehu yaxo ya dawo da sumy gida.. Kursum ta tashi sai dai ba ihu yanxu sai kuka kawai take, doctor ya shigo yana gayamata ai kawarta da sukai accident tare ta rasu dan haka yanxu ta shirya kanta dan kanin mamanta yazo daukanta suje gida, ya dauko wallet da pictures din yabata hade da jakan gabadaya sannan ya bata magunguna wanda zata sha, yace sumy ki tabata kinsha maganin nan saboda your body is still weak, tace to nagode sosai doctor, Kursum kam hankalinta duk ya tashi shikenan sumy ta rasu yanxu ya zata yi , gashi kuma ana tunanin itace sumy alhalin kuma sumy ce ta rasu ba kursum ba, amma kuma dole ne ta tsaya a matsayin itace sumy kodan ta samo wa hanifa gata da yancin ta. Ta fito ta iske baba shehu na jiran ta, dukda batasan shi ba saida tace kawu ina wuni, ya bita da kallon banza sannan ya amsa a kwasale yayi gaba abunshi tana binshi a abaya, a zuciyan ta tace tab wato family dinnan babu sauki, lailai zata daura damara dasu dan kuwa baza tai tolerating ko wana nonsense ba. Suna isa gidan yayi parking mota suka fito, masha Allahu kawai take fada dan kuwa bata taba ganin katon gida mai kyau kaman wannan ba, wani tausayin sumy taji, Allah yaji kanki kawata kuma insha Allahu hanifa sai ta samu gatan xaman gidan nan Daram. … Hajiya da xee suna zaune a parlour suna jiran isowan su sumy, baba shehu yafara turo kofa sai kursum abaya, tana karasowa cikin palon xee da mum suka tashi tsaye afirgice suna kallon ta……. Nima afirgice nayar da biron rubutuna dan na tsorata da yanayin mom, ita da bata gani miyasata firgita haka..:oops::oops: *Xarah Bêê* *Dedicated to Bady social* ~Luv u all~ kursum 36 to 50 Posted by XARAH ABUBAKAR on NOVEMBER 13, 2016 KURSUM By ~Xarah Bukar Page ~ Kursum ta dukusa har kasa ta gaishe su, hajiya kam hankalinta bai tare da ita, mamaki kawai take yadda sumy ta zama kekkyawan budurwa dan koda tasan ta abaya ba wani kyau garetaba sai fari kawai …….abangaren xee kuwa faduwan gabanta sai karuwa yake, yaudai duk takama da kyawuta taga Wace ta fita kyau da komai, wani irin tsanar kursum taji azuciyanta. …….:evil::evil: Hajiya amsa adakile, ta kwallawa samira kira, taxo da sauri tana gani hajiya, tace kikai sumy can gidan baya kusa da dakin masu aiki sai ta zabi dakin data ke so, samira tace toh. Kursum da haushi hajiya ya isheta ta, ta karaso cikin palon ta xauna tace tunda gidan ubana ne babu wanda ya isa yasani xama dakin masu aiki, dan haka nima a main house zan zauna, ta tambayi samira ina dakuna suke da kuma wana dakine yafi kyau da girma a gidan, tace antee dakuna asama suke kuma dakin daddy yafi kyau da girma tunda ya rasu babu wanda ya shiga, kursum ta mike tsaye ta karewa hajiya da xee kallon sannan tace samira kaini dakin daddy dan yanxu yaxama nawa in ga wanda ya isa ya hanani…:? Hajiya kaman tafasa ihu dan takaici, lailai yarinyan nan wato ba kyau kadai takara ba harda baki tayi, yazama dole insa mata ido saboda….. Da daddare Abba da umma ke zauna a parlour sai hira suke suna darawa, umma tace gaskia yakama in leka hajiya mun dade bamu haduba aiki yamin yawa. Abba ya kalleta yace wai ke bana hanaki shiga harkar hadiza ba, kinsan sarai banason matan nan saboda Sam bata da mutunci, kowa yasan itace sanadiya mutuwan mijinta , umma tace haba alhaji ya za ai kace haka, lokacin mijinta ne yayi……. bata ida magana na ba yazid ya shigo da sallaman sa, sanye yake da uniform dinsa na pilot wanda ya kara fito da ainuhin kyau shi, ya fada kan kujera yana wai na gaji, umma ta kalle shi tace my son hope dai you are okay, banason ganinka da stress , Abba yayi tsaki yace wlh maryam ke kike kara sangarta yaron nan, idan baije aiki ba so kike yana xaman gida ko me, shida wataran zaiyi aure ya kula da iyalansa……yauwa nama tuna shehu yazo min da batun diyar shi Zainab dinnan kwana kin baya, kun dade kuna soyyaya amma baka ma xancen aurenta kuma ma dai at your age ya kamata ace kafara tunanin fara iyali. Yazid ya tamke fuska, yace gaskia abba ni ban shirya aure ba dukda inason xee, koda zanyi aure sai nan da shekera daya, ya tashi a fusace ya wuce dakin shi. Abba ya kalli umma yace kinga halin son dinki ko , tace karka takura mai tunda yace ba yanxu ba, ni xee dince ma banaso ya aure Sam bata da kamun kai, yace to ina ruwanki bashi ya gani yanaso ba kuma ni banga rashin kumun kan taba, babanta abokina ne kuma yana da kirki sosai, umma dai shiru tayi bata ce komai. *************************** Bayan kwana biyu jikin kursum ya warware ta samu sauki sosai tayi fresh ta kara kyau, sai dai zaman kadaice da take babu mai shiga harkanta a gidan sai samira kawai dan ita ke kawo mata abinci har daki, tayi tsaki ta kwallawa samira kira, taxo da saurin ta tace antee kina bukatan wani abu ne, kursum tace babu komai tambayan ki zanyi wai babu masu shigowa gidan nan ne, naga tunda na zo banji an shigo ba, gida sai kace kurkuku……samira ta gyara zama tace antee ai indai gidan nan ne ana wata biyu babu wanda ya shigo, yaya yazid kadai ke xuwa wataran umman shi takan zo wajan hajiya dan kawarta ce sosai, kursum ta nisa tace Waye kuma yaya yazid wajan wa yake zuwa, samira tace ai saurayin antee Zee ne kuma suna son junan su sosai bare ma antee zee tana iya mutuwa akanshi, kursum ta bata rai tace tashi ki fita ban tambayi ki wannan ba, sumsum ta tashi ta fice da saurinta……ita ko wani farin ciki taji ta maimaita sunan yaya yazid, gaskia sunan ya mata dadi. .. :mrgreen::mrgreen: Da yamma barrister shu’aibu yazo har gidan ya damkawa kursum takardun gidan da komai data mallaka amatsayin itace sumy, sannan yace mata ta shirya gobe zata fara aiki acompany din babanta amatsayin managing director, tamai godiya sosai ya masu sallama ya fice. Hajiya dake gefe sai hararan kursum take ta eye glass dinta (oho dai batasan kina yiba)…… Baba shehu ma ya cika yayi fam , ya kalli kursum yace yanxu sumy abunda ya kamata shine kibarmin komai a hannun na tunda na dade in charge, xan naima maki admission ki shiga university tunda iya kacinki secondary skull kuma baki da experience na managing babban company, kursum shiru kawai tayi batace komai ba ta haura sama abunta. …. Baba shehu yayi murmushin samun nasara da alaman yarinyar ta yadda da Zancen shi….:mrgreen::mrgreen: Washe gari da safe kursum ta shirya cikin hadadden pink and white suit mai shegen kyau na kardashian collection tayi rolling kanta da karamin pink veil mai kyau, ta dauki handbag karamin mai kyan gaske mai tambari versace tarike a hannu, tabi stairs tana sauka atsanake hankalinta kwance, ji tayi an bangajeta har tana naima fadowa kasa, tana daga kai tayi ido hudu da xee, da ganinta kasan she is high danko kayan jikinta bana kirki bane, xee tace ke dabbar ina ce ko bakiga ina hawowa bane, banza bakauya taja tsaki ta wuce, kursum kasa cewa komai tayi ta wuce abunta tana mamakin hali irin na xee ta tabbata daga club take kuma till dawn tayi, dan samira ta taba gayamata xee bata fiya kwana agida ba, bata da aiki sai clubbing, kuma baba shehu da hajiya suna sane amma babu mai kwabarta…. Allah ya shiryeta kawai tace ta karasa waje ta shiga hadaddeyar motar ta kirar 2016 Buick Cascada……….driver yaja ta sai company. Babban Company ne mai huge twenty-story office building, all curved glass and steel, an architect’s utilitarian fantasy, with Tanimu bawa oil & investment written discreetly in steel over the glass front doors. Tana shiga officials din suka karaso suna gaishe ta tare da mata congrat as the new MD , ta amsa da fara’arta tana masu godiya, Mr dabo ya karaso gabanta yace madam am your PA let me excort u to ur office, ta bishi har office din amma sai tayi mamakin :oops::oops: ganin office karami kaman gidan kaji, ta juyo tace Mr dabo how comes ina MD zaa bani karamin office haka, yace madam kiyi hakuri ba laifin mu bane, kawunki yace abaki nan tunda ba wani sanin kan aikin kikayi ba, kursum tace lailai ma baba shehu wato itace ta dace danan, aikuwa zanyi maganin shi…. ..tace Mr dabo kaini office din baba shehu yace toh… Suna shiga taga office dinshi tankameme kaman aljarnar duniya komai na office din ya burgeta tace Mr dabo nan nake so as my office ka kwashe tarkacen kawo ka canza mai wani office sannan kuma ka kawo min file din ko wana employee zan fara aiki na, yace to angama madam Ya fice. … Kursum zauna kan office chair tana swivel din kanta, sumy kawai take tunanin, Allah sarki kawata da yanxu kice anan bani ba, Allah yaji kanki insha Allahu zan rike maki hanifa tamkar nina haifeta… Banko wan kofan da akayi ne ya firgita ta, baba shehu ne fuskar nan tamke, babu annuri ko kadan, yace “I won’t let you disrespect me, I’ve been working day, noon, and night for this company, busting my hump since before you were born.” who are you to throw me out of my office? Kursum ta mike tsaye ta karemai kallon sannan tace, the early bird doesn’t always catch the worm, Warming a seat in this company doesn’t mean you’re working, baba shehu daya gama kulewa ya nunata da yatsa yace, how dare you, you snot- nosed brat! Kinsan dawa kike magana kuwa, ta kara kare mai kallo tace, I dare because I’m the heir to my father’s company. From now on, I’m going to monitor the performance of every employee; including you. No, not including, but beginning with you. If you don’t like it, the door is wide open enough. Understand? or should I draw you a picture?” Baba shehu kasa cewa komai Cox kalamanta ba karamin girgiza shi yayi ba, sai yanxu ya tabbatar kawar da yarinyan nan will not b easy, amma dole ne ya naima mafita kafin taza ma doom dinshi Hmmmm *Xarah Bêê* *Dedicated to Bady social* ~Luv u all~ KURSUM By ~Xarah B Page ~ Zaune yake a office dinsa yana waya da xee tana ta zuba mai shagwaba kaman tana gabanshi, ta turo baki tace baby kace zaka zo Jiya baka zo ba I couldn’t sleep Cox I was thinking of u kuma your fone was off, ta kara shagwabe fuska, yace am sorry dear I was kinda busy ne xanzo anjima, kar kiyi fushi kinsan I love you alot……….Abba ne ya shigo office din yasamu kujera ya zauna jiran ya gama wayan, yazid yace baby xan kiraki later, tace toh my love, kisses & hugs dear …… Abba yace miye amfanin love dinnan da bai da future, ance kayi aure kace you are not ready, kudai yaran zamani halinku sai ku, yayi murmushi yace abba abar xancen auran nan plz, nace muku am not ready, abba yace kai ka sani yanxu dai ga document din shares din mu na Tanimu bawa oil & investment company, Ina so gobe ka kaiwa new MD na company din tasa hannu, ya dire mai document din ya fice abunshi , yazid ya bude yana dubawa yace abba kenan wato dan aikin nan ma bazai tura wani ba dole dai ni zai aika……..:evil::evil::evil: Hajiya ce zaune a falo rike da sandar ta, tasha bakin glass dinta, tunanin kawai take yadda za ta fidda sumy daga gidan dan Sam bata yarda da ita ba, tana suspecting akwai abunda take boye masu, tasha leka dan karamin ramin dake jikin kofan dakin ta, ta ganta rike da wani hoto tana kuka tana cewa ki yafeni hakan da nayi shine kadai mafita, hajiya ta tashi da saurin ta haura sama, ita dai tana son sanin wana mafita sumy take nufi, ta bude dakin kursum ta shiga ta fara bude bude da binciken amma bata ga komai ba, side drawer na gadon taxo budewo ta ji muryan samira abakin kofa tana cewa Antee kin dawo ne, da sauri ta maida glass dinta ta fito daga dakin, samira tace hajiya kece aciki ashe, ko kallonta bata yi ba ta bi gefe ta wuce tana dafa bango dan karta fadi…….. Samira mamaki ne ya cika ta, matar da bata gani miye na shiga dakin daba nata ba kuma da alama ma bincike take, ikon Allah kenan…..:oops::oops::oops: Kursum zaune a office tana hada files waje daya dan yamma tayi zata wuce gida, ta kira Mr dabo tace mai ya kwashe duka files din ta gama dubasu sannan tamai sallama ta wuce parking lot tasamu driver na jiranta a mota, ta shiga ya ja…. Sun hau kan babban titi driver ya hango hold up sosai, babu alaman motoci na motsi, yace madam hold up dinnan yayi yawa amma akwai wani one way gaba kadan, bari inbi damu tanan, kursum tace toh duk yadda kayi ta cigaba da kallon sabuwar wayar da ta siya dazu kirar iphone 3G king’s Button… Daidai lokacin da driver ya danno kan motar, dai dai lokacin da shima ya karyo kwana sai ji kake kiiiiiiiiiii……..ko wannan su yaja birki, kiris ya rage suyi accident.. Sanye yake da uniform dinsa na pilot yasha kyau da alama shima daga aiki yake ya fito fuska tamke, tun kafin ya karaso driver ya fito da sauri yazo yana bashi hakuri, amma ina shi kam baisan hakuri ba sai zazzaga masifa yake yace kai wawan ina ne, koka taba ganin inda akabi one way, hanyar da ake fita shine kake shirin shiga tunda baka da hankali, driver dai sa hakuri yake bashi…. Tana daga mota take jin hayaniyan su, wato driver na bashi hakuri shi ko guy din kara harzuka yake, lailai ko zata yi maganin shi, ta bude kofar motar ta fito da tafiyar ta mai daukan hankali ta karaso ta bayan shi tace Mr man ko Kaine devil himself sai haka, ana baka hakuri kana kara harzuka, toh karka hakura idan titin taka ce sai mu gani, taja uban tsaki, ya juyo a fusace fuskan nan ba annuri, ya kare mata kallo tas yace ni kike gayawa wai maganar banza , ita ko hankalinta bai ma jikinta dan ba karamin tsorata tayi ba, tabbas babu tantama wannan shine wanda sumy ta aura ya yaudare ta ya gudu, sau daya ta taba ganin shi amma bazata taba manta wa da fuskan shi ba, ba shiri ta saita kanta, ta wurga mai harara tace kwarai kuwa dakai nake kai din banza Waye kai da bazaka hakura ba, Driver mu tafi plz karya hakura din yana iya kwana anan tunda hanyar tasa ce, ta juya ta barshi nan tsaya yana mamaki karfin hali irin nata, lailai ko sai ya koyawa mata hankali, ya ga ubanwa ya tsaya mata da har ta isa ta gayamai magana, yayi kwafa yaja motar sa yabar wajen. Suna cikin mota tana tunani iri iri, gaskia dole ta naimo Mr devil kodan ta koyamai hankali, wato hankalin shi kwance har wani kyau yakara, kibiyar tsanar shi ce ta soki zuciyar ta, tayi murmushin mugunta afili tace count down to my revenge has ended, it’s time for pay back Mr devil…… Driver yace madam mun iso fah naga kinata magana ke ka dai, tace ahh ba komai barin sauka saika gyara parking, yace toh. Ta turo kofar parlour da sallaman ta, hajiya da xee na zaune ko kallo bata ishe su ba, tana gaishe su ko amsawa basuyi ba suka bita da harara, ta haura sama abunta…. Xee da taci uban kwalliya da wasu matsasu kayan dake jikinta, ta kalli hajiya tace ni wlh na tsani yarinyan nan ga shegen kyau kamar aljana, ni wataran kina min kama da ita ma, hajiya taja tsaki tace ke daina hadani da mayya ni kaina na fiki tsanar ta, na gayamaki tsinto ta Alhaji yayi a titi, ko jini ban hada da ita ba……..zata kara magana hajiya ta tsayar da ita, tace surutun ki ya isheni haka, ba kince saurayin ki zai zo ba, toh sai kiyi zaman jiran shi ai, nikam na tafi daki……xee tace haba hajiya ki tsaya ku gaisa mana, tace nikam bacci zanyi ta haura sama abunta. Tun komawar shi gida, sallah kawai ya iya gabatarwa, ya rasa inda zaisa kanshi yaji dadi, abunda ya faru dazu gani yake tamkar a mafarki, wai yau shine little witch (sunan daya laka mata ) tama rashin M, lailai ko saiya making life dinta miserable sai tayi dana sanin cin zarafi da ta mai, wani irin tsanar ta yake ji, ya mike ya naushi bango a fili yace Game on little witch……….:evil::evil::evil: Hmmmm tashin hankali Masu karatu muje xuwa….. (Dedicated to Bady social KURSUM by ~ Xarah Bukar Page ~ Tana shiga dakin ta ganshi a hargitsi da alaman an shigo an mata bincike, ta kwallawa samira kira, taxo da saurinta tana antee har kin dawo kenan, kursum tace waya shigo min daki naga komai ba daidai ba, samira ta sosa keya tace Antee nima bansani ba amma dai naga hajiya ta fito daga dakin dazu…. Kursum tace hajiya kuma, ita da bata gani miya shigo da ita dakina, tayi shiru can dai tace tashi ki tafi zan naime ki anjima, samira ta tashi ta wuce….. Ta tashi ta gyara dakin ta kimtsa komai daidai , sannan ta bude side drawer ta dauko picture dinta ita da sumy da pink diamond dinta wanda su kadai ta tsira dasu ranar da sukayi accident da yake cikin aljihun trouser dinta tasa su, ta kalli pic din tana hawaye, rayuwarta da kawarta kawai take tunawa, tayi missing dinta sosai , yanxu tunanin ta daya shine yadda zata dauko hanifa daga Bauchi, ta tashi ta dauko wani karamin book din sumy inda Inna sadiya ta rubuta masu number ta akan in sun iso zasu kira ta, da sauri ta kwashe lambar tayi dialling………ringing daya biyu Inna sadiya ta dauka da sallaman ta, kursum tace Inna ina wuni ya gida, ya hanifa, nasan baki gane mai magana ba kursum ce…..Damm gaban Inna ya fadi gaba daya ta gigice dan bata taba tunanin kara jin muryar kursum ba, tace kursum dama baki mutu ba , aini dana je aiki makaranta gimbiya ke cemin ai kunyi hatsari kin rasu, kursum tace eh wlh munyi hatsari amma sumy ce ta rasu bani ba. Inna tace Allah yaji kanta, yanxu hanifa ta zama marainiya, kursum nace haba Inna kar kice haka, nice uwar hanifa yanxu bazan taba bari tayi maraici ba, insha Allahu dana samu lokaci xanzo in dauke ta, Inna tace to babu damuwa sai kinzo, gatanan kuwa tayi bubul da ita, kursum tayi murmushi tace Inna karki gayawa gimbiya ban mutu ba, kibarta amatsayin ni na rasu ba sumy ba, Inna tace toh duk yadda kikace, sukayi sallama ta ajiye wayan….. Driving yake hankali kwance, fuskar shi ba yabo ba fallasa, yasan rigimar zee idan baije wajen taba zai sha mita, ya iso gidan mai gadi ya bude mai gate ya shigo ciki…… xee data cika tayi fam a parlour, sai tsaki take ja, wajen awa hudu kenan tana jirashi ta kira layin shi switch off, ranta duk abace:evil::evil::evil: taji karar doorbell , ta kira samira taje ta duba waye, ta bude ta ganshi tsaye yana mata murmushin, tace yaya yazid sannu da zuwa ashe Kaine, yace yauwa samira ya karaso ciki, tana jin muryar shi ta tashi da sauri tana kukan shagwaba taje ta rungume shi. yace haba zee kukan mi kike haka, ta kara fashewa da kuka tace ba Kaine kaki zuwa ba tun dazu nake jiranka, yace baby kiyi hakuri yanxu nazo ai forgive me ? Kinji baby na yakara rungumeta tsam yana shafa bayanta, ita ko sai sauke ajiyar zuciya taje.. Basu ankara ba sai ji sukayi ana tafa masu lokacin guda suka saki juna suka juyo suna kallon ta, sanye take da black jeans da yellow top, sauko wanta kenan zata je kitchen ta naima wa kanta abun ci ta gansu makale da juna kaman ba gobe…. ta masu kallon up & down, tagane guy din sarai shine Mr devil wanda suka samu clash dazu, tace lovers of the year duk iskanci da kukeyi awaje bai ishe ku ba har sai anxo ana nuna hali a gida:?:?, shi kam yazid kasa magana yayi dan mamakin ganinta yake for d second time kuma a gidan nan, ta karaso gabanshi ta nuna shi da yatsa tace shameless man haka dai zaka kare da bin mata, dan iska kawai, xee data bata rai jin kalaman da kursum take gaya masu yasata karasowa da niyyan wanketa da mari amma ina kafin takai mata marin kursum ta rike mata hannu gam tace don’t you dare sis, jikina yafi karfin duka, kuma am advicing you to stay away from diz man cox he is just using you for his own selfish reasons, tayi tsaki ta wurgar mata da hannun ta wuce kitchen abunta….. yazid yace baby ina kuka samo witch dinnan ne, I hate her with passion, she is rude, zee tace diyar daddy da hajiya ce, shegiyar yarinya, mayya, Yar titi, agidan marayu daddy yasa mota, tana school ne sai yanxu ta dawo gida ……:? ya nisa yace baby barin wuce kawai, am not in a good mood, tace haba yaya daga zuwan ka zaka tafi, indai akan abunda ta fada ne kayi hakuri zan mata magana , yace sorry zee but I have to go, ya mata peck a cheeks ya wuce rai abace:evil: kursum da take hango su ta kitchen ta kara mata rai, ko miye na mata peck kuma in ba iskanci ba, zuciyar ta namata zafi …… (su kursum da karfin hali, mutum da budurwa shi karya soye ) *Xarah Bêê* kursum 51 to 52 Posted by XARAH ABUBAKAR on NOVEMBER 13, 2016 KURSUM by ~ Xarah Bukar page Abincin ma kasa Ci tayi dan haushi, ta fito zata wuce dakinta zee ta finciko ta, tace ke yar titi ki fita daga ido na, ke har kina da bakin Kiran mutum dan iska, wayasan iskanci da kikayi a makarantar da aka jefar dake, ina baki last warning ki fita daga rayuwa ta…… kursum bata ce mata komai ba illa gyara rigarta da tayi ta wuce abunta, zee tayi kwafa tace lailai ma yarinyan nan, ya zama dole in binciki past dinta, xanje har makarantar da aka riketa in samu wani abu akan rayuwarta. … umma ce zaune a daki tana duba new designs dinta a laptop, yayi sallama ya karaso ya fada kan gado, tace my son daga ina haka a darennan, naga ma ranka abace, hop all is well ? yace ba komai dama wajan zee naje, nan take umma ta bata rai, ita dai bata kaunar zee ko kadan, dan farin cikin son dinta take nuna tana sonsu tare, ya nisa yace umma dama hajiya hadiza nada ya’ budurwa ?? Dam gaban umma yafadi dan tasan tabbas hadiza nada diya kuma yanxu ta isa zama budurwa, tace my son hajiya bata da diya tun wajan haihuwa yar’ta ta rasu, nasan dai alhaji yayi adopting yar yarinyar daga gidan marayu, zaman su yaki dadi da hajiya shine yakai ta wani boarding skull…. yazid yace ta dawo ai, ita nagani a gidan dazu, yarinyar sai rashin kunya da raina mutane, umma tayi dariya tace haba son daga ganin yarinya sai aibata ta, Allah umma dagaske nake sau biyu muna haduwa tana min fitsara, sam bana sonta:?:? umma dai dariya kawai take yadda ya dage shi baya sonta, sai kace ance ya so ta, tace son abbanka ya wuce England dazu, yayi trying line dinka switch off, yace eh wlh I was so busy ne, zan kira shi gobe, tace to yace dai karka manta gobe ka kai ayi signing document din daya baka dazu, yace toh umma barin je in kwanta good nyt, okay nyt my son. ******** sauri take ta wuce office dan yau ta makara kuma suna da meeting, harta fito daga daki ta kara komawa da sauri, ta bude side drawer ta dauko pink diamond dinta, tayi murmushi, ta san koba komai tana da abunda uwarta ta ajiye mata, ta saka pink diamond din jikin chain din wuyanta, ta fito tayi kicibis da hajiya abakin kofa amakale tace hajiya ina kwana, mai kikeyi abakin kofana ? kina son wani abune ?? lokaci guda take jero mata tambayoyi, hajiya data gigice ganin diamond din wuyanta yasata fara kame kame, tace daban kwana ba zaki ganin, shegiyar yarinya toh wuce wa xanyi ta wuce fuuuu har tana naiman faduwa, kursum dake tsaye tana mamakin hajiya, anya matan nan bata gani kuwa, ta rufo dakin ta wuce. hajiya ce a daki sai sake sake take da tunani iri iri, ina yarinyar nan tasamu diamond din nan, nasan ni kadai keda irinshi kuma na bayar dashi dadewa, wayarta ta dauko tayi dialling line din mairo dan tasan ita kadai ce zata bata amsar komai, ringing daya umma ta dauka, kafin ma su gaisa hajiya tace mairo kizo gida inason ganinki, ina son muyi magana akan abunda ya faru shekara goma sha takwas da suka wuce…… Dam gaban umma ya fadi, :oops::oops::oops:dama tasan zaa rina. *Xarah Bêê* *Dedicated to bady social* KURSUM by ~ Xarah Bukarêê page Tana isa boardroom ta wuce, “suka fara meeting, dama ita kawai ake jira, “baba shehu sai zuba bayani yake, ita dai bata gane komai ba har aka gama, ta koma office dinta. baba shehu ne yashigo office din, sai wani fara’a yake kaman dagaske, “kursum tace baba da kanka, ayda ka turo wani, yace “nida ya’ta ai dole inzo gaisheki da kaina, ya mika mata check din makudan kudi tayi signing, ta karba ta duba tace “baba kudin sunyi yawa, me xaai dasu ? “ya sosa keya yace dama wasu sabbin machines na company mukeso importing dan wanda muke dasu sun fara lalace wa. tace toh shikenan amma dai xan rage kudin sunyi yawa, tayi signing ta mika mai, bai ji dadin abunda tayi ba ya amsa ya fice rai abace, ita dai kursum bata yadda da fara’arsa ba kwanan nan sabanin da idan ta gaishe shi sai harara da zargi yake wurgo mata. zaune yake a office yana duba takardun dake gabanshi, can ya hango papers din shares dinsu da abba ya bashi yakai T. b oil & investment company asa hannu, da sauri ya mike ya kwashe papers din tare da car keys dinshi ya fice Da sauri yake driving har ya iso company din, ya tambayi daya daga cikin workers din inda office din MD yake, suka kai shi office din Mr dabo, da sauri mr dabo ya tashi ya gaishe shi dan yasan family dinsu ne major share holders din company din, “Yazid ya bashi hannu suka gaisa dan ya sanshi sosai mutumun abba ne, “yace mr dabo ashe kaine new MD din, dabo yayi dariya yace ai bankai matsayin nan ba, nine dai personal assistant din new MD din, barin gayamata tayi bako, da sauri ya fice ya dawo yace kana iya ganinta yanxu, “Yazid yace okay thanks….. Hankalin ta kwance sai buga game take abunta, yayi knocking kofa, ko dagowa batayi ba tace come in, yana karaso ciki ya ganta yaji mugun takaici, dama witch dinnan itace MD din, lailai ko yau idan tamai fitsara bazai barta ba, bai ankara ba yaji tace can I help you ? ya kara kallonta wato ko dagowa baza tai ba game dinta kawai take, lailai ko zanyi maganinta. …… Papers din hannun sa ya watso mata a fuska, da sauri ta dago suka ido, sai da gabanta ya fadi dan ba karamin kwarjini ya mata ba, ta harare shi, ta daure tace “miye haka zaka watso min papers, have u lost your manners ? ya bata rai, “yace aiki kika zoyi ko game, ko an gayamiki wasan yara ake anan, ta murguda baki tace “bansani ba ina ruwanka, dariya ma ta bashi, yace “signing zakiyi akan papers din” ta yamutsa fuska tace na miye , harara ya wurga mata yace baki iya karatu bane, “ta hada papers din waje daya ta karanta ta kalle shi tace “ashe kuna da shares a company dina” yayi banza da ita , tayi murmushi ta tashi ta karaso gaban shi ta ajiye mai papers din tace ” banda pen ( biro) balle inyi signing, kana iya komawa da papers din, next time idan xaka zo saika hado da pen ta zauna taci gaba da game dinta… Bai ji haushi abunda tace ba, ya tashi yadau papers din yai murmushi ya kalle ta yace” I have nothing to say amma keda kanki zaki ne me papers din, ya fice daga office din. Mr dabo ne yashigo office din da saurin sa yace madam lafiya dai koh, naga bakonki ya fita a fusace, ta yatsine fuska ta gayamai abunda ya faru, yace “madam ai kinyi kuskure babban saboda sune major share holders din company dinnan, idan suka kwashe shares dinsu company dinnan zai zama bankrupt kuma zaiyi affecting oda share holders, “kursum da hankalinta ya tashi tace mr dabo yanxu ya xaai kenan dan papers din na hannu shi, “yace abu mai sauki tashi zakiyi muje har office dinshi ki bashi hakuri ya baki papers din, “tace to muje ” handbag dinta ta dauka da sauri suka fice… umma ce ta shigo parlour gidan da sallaman ta, shiru babu wanda ya amsa “can ta hango zee zaune tana kallon tv da alama batasan ma ta shigo ba, ta karasa ciki tace baki ji ina sallama bane , ta juyo ta kalle ta aya tsine tace banji bane sorry, umma tare kuke da yaya yazid ? umma tayi banza da tambayan tace ina hajiya ? zee tace bansani ba amma ki dubata sama, ta cigaba da kallon tv abunta. …..Umma tayi kwafa ta haura sama, tana takaicin hali irin na zee, sam batayi sa’ar suruka ba. hajiya ce zaune a daki sai kuka take tana dana sanin jefar da yar’ta datayi, babban tashin hankalinta shine rashin gayawa daddy cewan yar’su bata mutu ba harya rasu, kuka kawai take tana dana sanin bakin halin data shuka a rayuwarta, “da sauri umma ta karaso wajanta tana hadiza lafiya, meke damunki ? hajiya tayi shiru tana tunanin yadda zata gayawa umma ta ga pink diamond dinta awuyan sumy, saboda kowa yasan makauniya ce, ta nisa tace “shekarun baya da suka wuce nayi niyyan jefar da ya’ta, amma kika dauketa kika kaita inda zaa raineta harta girma, “ta kara fashewa da kuka tace mairo ina ya’ta kursum take ? kina da labarinta kuwa ?? umma ta gyara zama tace “hadiza ni bansan inda yarki take ba, makarantar dana kaita munyi dasu idan takai shekara sha takwas zasu sallameta, kuma yanxu ko ta cika sha takwas dan gimbiyar makarantar ta kirani ta gayamin tacika alkawarin dake kanta na bawa yarinyar diamond din da kika ajiye mata. … agigice hajiya ta kalle ta, tace mairo ki taimakeni ki kiramin gimbiyar awaya, ko zata San inda ya’ta taje ranar da suka sallameta, umma tace to barin kirata muje, dan nima tunda nakai yarki makarantar ban yanke zumunci da gimbiyar ba, dan nasan wataran zaki nima yarki….. Tasa masu call din a speaker, ringing daya biyu Gimbaya hafsatu ta dauka da fara’arta, suka gaisa da umma, “umma tace dama zancen kursum ne, ko kina da labarin inda take yanxu, gimbiya ta nisa tace “ai kursum Allah yayi mata rasuwa tun lokacin da muka sallame ta, kawarta tabi suje gidansu a kano shine sukayi hatsari a hanya, ita ta rasu amma kawar bata rasuba, “Dam gaban hajiya ya fadi, shikenan yar’ta ta rasu” umma tace gimbaya ya sunan kawarta ? tace sumayya tanimu bawa sunan ta, umma tace nagode sosai gimbiya sukai sallama. Rudani, tashin hankali, lokaci guda hajiya ta shige su, ta kalli umma da jajayan idonta da suka rine tsaban kuka tace “babu tantama sumayya gidan nan ce kawarta, tare sukayi accident kursum ta rasu, kuka kawai take tana salati , taga samu taga rashi, “umma sai bata baki take tana kwantar mata da hankali, amma ina kuka take , bata ankara ba sai gani tayi hajiya ta fadi kasa sumammiya. :oops::oops::oops::oops::oops::oops: Xarah Bêê kursum 53 to 55 Posted by XARAH ABUBAKAR on NOVEMBER 13, 2016 Kursum by ~ Xarah Bukar page Umma ta tashi ta dibo ruwa ta yayyafa mata, amma shiru hajiya bata tashi ba, a gigice ta fito ta kwalla wa zee kira, zee tazo da saurinta tana “umma lafiya kuwa?? tace ba lafiya ba maza kira doctor malik, hajiya ba lafiya, “da sauri zee tayi kiran layin doctor tana gayamai abunda ya faru, “doctor yace ni yanxu am very bixy , zan turo ambulance yanxu akawo ta asibiti, “zee tace toh dr. muna jira. Ba’a fi minti biyar ba, ambulance yazo suka wuce asibiti gaba daya, direct emergency aka wuce da ita, umma da zee na daga waje hankalinsu duk atashe, umma tace zainab kin gayawa shehu muna asibiti kuwa? , tace eh yanxu na kira shi yana hanya zuwa ma, “umma tace tun dazu nake trying line din yazid ban samu ba, gwada kira min shi ko zaki samu, “zee tace nima dai tun dazu nake trying line dinshi ban samu ba, amma barin je office dinshi inji ko lafiya, umma tace toh ki gayamai ina naiman sa yanxu nan, tace to ta wuce. Zaune yake a office yana sipping coffee, yana danna laptop dinshi hankali kwance, ya dauka papers din ya kare masu kallon, yayi murmushi ya ejiye su gefe, secretary dinshi suzzie ta shigo, “tace sir a lady is here to see you, “yace owkay tell her to come in” suzzie ta fita tace madam u can go in, kursum tace tnx, ta juyo ta kalli Mr dabo “tace karna batama lokaci, kana iya komawa office, idan nagama zan naimi taxi indawo, yace toh madam sai kinzo, ya wuce. Ta turo kofan tashigo, wani irin kamshi mai dadi da sanyi suka mamaye ta, offfice din mai girman gaske dan har yamafi nata, dago wa yayi ya kalleta yayi murmushi ya cigaba da abunda yakeyi, “ta karaso tace mai sannu taja kujera zata zauna, ya dakatar da ita yace “baa zaman min a kujera saida izini ni na, kuma miya kawo ki nan?? Tayi shiru ta koma gefe ta tsaya, “tace humm mm dama papers dinnan zaka bani inyi signing” yayi banza da ita kaman beji abunda tace ba. Har kusan minti biyar baice komai ba kuma bataga alaman zaice ba, ga tsayuwar ta isheta daurewa kawai take, “kashe laptop din yayi ya tashi ya dibi wasu files, ya kalleta yace kina iya zaman a couch din can kiyi game din da kikasaba, ni yanxu ina da important meeting da zanyi attending” bai jira abunda zata ceba ya fice. Ba yadda ta iya dole ta jira shi, ta bude jakanta ta dauko wayanta ta fara game, har kusan 30mins bai dawo ba, gashi ta gaji da game din, ta kwanta ta fara bacci abunta, “bayan awa daya ya shigo ya cigaba da aikin gaban shi, yama manta da wata a office din, can ya dago zai dauki wasu files ya hango ta kwance kan couch tana bacci da alama ma sanyi Ac yamata yawa dukta takure waje daya, ya dauki papers din ya taso zuwa wajenta da niyyan ya tashe ta, ya tsugunno setin fuskan ta yana kallonta, yaune na farko daya kare mata kallo, ya ciro wayan shi yayi snapping dinta, ta gyara kwanciya veil din kanta ya zamo kasa, gashin kanta ya zubo ya rufe mata kakkyawan fuskan ta, da sauri yasa hannu ya matsar da gashin gefe, karaf ta tashi sukayi ido hudu dashi, ya tsakar mata lausassar murmushi, “ta lumshe ido tana kallonsa wani irin sanyi take ji azuciyar ta, dakyar ta mike, ta Harare shi “tace miye haka zaka tabani? ? Dariya ma ta bashi, ya mika mata papers din yace kiyi abunda kika ga dama dasu, ta bata rai ta amsa ta ciro pen a jakarta tayi signing ta mika mai, ta tashi tace sai anjima, yace “babu ko godiya, tayi banzan dashi ta wuce zata fice, takasa bude kofa, ta danna lock din yaki budewa, ta juyo ta kalle shi a fusace tace “nakasa bude kofan, yayi dariya ya taso yace d door is open kece dai yar kauye baki iya budewa ba, yasa hannu xai bude kenan aka bango kofan daga waje kursum ta fada jikin shi a tsorace:oops::oops::oops: Zee dana gama kulewa ganin kursum jikin masoyinta yasan ta kara fusata:evil::evil:,tace yaya yazid dama shegian yarinyan nan ce a office dinka tun dazu, shine secretary dinka ta zauna dani office dinta tun dazu akan cewa kana da important visitor, gajiya nayi da jira shiyasa nayi deciding in shigo kawai, ta fashe da kuka Ya yazid kasa magana ma yayi dan haushi, dan dama haka take shigo mai office duk lokacin data ga dama,”kursum ta karaso wajenta da sauri tace “kiyi hakuri, wlh ba abunda kike tunani bane, aiki ne yakawo ni nan ba komai ba” zee ta Harare ta tace karya kike munafuka dama daga ganinki ke yar bariki ce, mayya yar titiiiii…….bata ida magana ba ya yazid ya wanketa da mari saida taga wuta , tace baby ni ka mara? Yace namareki din, ba sister dinki bace atleast respect her for once, “kursum dai tana gefe bata ce masu komai, zee tana kuka tace baby dan ina sonka dayawa shiyasa kakemin wulakanci, ta kalli kursum tace ke kuma hajiya na asibiti ba lafiya kinzo nan kina cin amana, toh baki isa ba kuma sai na koya miki hankali ta fice , da sauri itama kursum ta bita tana kwalla mata kira. Yana nan tsaya yaji wayar shi na ringing ya duba yaga umma,da sauri ya dauka suka gaisa, tace my son I hav been trying ur line bai xuwa, kana ina ne? “Yace ina office umma, tace to kazo ka sameni a asibitin dr malik yanxun nan, hajiya hadiza ce ba lafiya, yace toh ganinan umma, ya ajiye wayan da sauri yadau mukullin mota ya fice. Har bakin mota ta biyota tana zee kiyi hakuri mana, ki taimaka ki kaini asibitin banzo da mota ba, zee tayi banza da ita ta shige mota abunta taja a fusace:evil::evil: Haka ta karaso bakin titi kozata samu taxi, shiru dai bata samu ba ga wani irin ciwon kai dake damunta, tana tsaye wata hadaddiyar jeep kirar classic 2020 taxo gabanta, yayi wining glass din motan, yace little witch shigo in kaiki, tayi banza dashi, yayita mata horn taki kulashi, da daga dai zai kara mata ciwon kai tayuwo tace ya yazid miye haka, nace bazan shigo ba ka wuce kawai, “yace asibiti zani wajen hajiya kema nasan can zaki je, kizo in maki lift dan bazaki samu taxi anan ba, ta tsaya tunani, ita dai bataso zee ta kara ganin su tare, haka dai ta hakura ta shigan motan. Har suka iso asibitin babu wanda ya yiwa wani magana, ta fito da sauri zata wuce ciki, yace ke kinsan inda aka kwantar da ita ne? Tace a’a, “yace to saiki jirani ai tunda ni nasan wajen, duk sai taji kunya, haka suka jero har inda umma ke zaune, ya karaso gabanta yace umma lafiya dai ko? Tace eh hajiyan ta farfado, yanxu bacci take ma, shehu yana wajen doctor jin meke damunta, kursum dake bayanshi ta karaso ta gaida umma da mata godiya sosai akan kokarin datayi na kawo mamanta asibiti, umma dai sai kallonta take dan batasanta ba, tace my son ina kasamo pretty girl dinnan, yazid yayi dariya yace ai sumayya ce diyar hajiya, na rage mata hanya ne,”umma tace ikon Allah dama ni ban taba ganinta ba, ya kike sumayya? Kursum akunya ce ta amsa tace lafiya kalau, umma dai sai murmushi take, ji take kaman tasan ta, wani irin son yarinyan taji har cikin zuciyan ta.:mrgreen::mrgreen: Baba shehu ne ya fito yasame su yake gayamasu ai jinin hajiya ne yahau sosai dalilin firgeta da tayi, dan yanxu haka ta farfado amma har yanxu tana tare da shock,”ya kalli umma yace haijya mairo bata gayamaki abunda ke damunta ba kafin ta suma, umma tayi shiru batace komai, baba shehu yace toh Allah ya bata lafiya shine kawai fatan mu, yanxu dai doctor yace mutum daya zai zauna da ita, inya so gobe mazo mu ganinta, ya kalli kursum yace ke kizauna da ita harta tashi, hajiya mairo kuna iya tafiya tunda sai gobe za’a iya ganinta, “umma tace to shikenan bari mu wuce, gobe saimu dawo, my son let go, ta kalli kursum tace sumayya ki kula da mamanki sosai kinji, tace toh umma zan kula da ita sosai. baba shehu yace zan turo samira ta kawo muku abunda zaku bukata,tace toh”ya wuce abun shi. Har sun wuce ya yazid ya dawo da sauri yace Karki zauna kina game, akula da marar lafiya dai, ta murguda mai baki tace ina ruwanka toh:?:?…… yayi dariya yace zanyi maganin tsiwan nan naki, ya fice da sauri…… Ta tura kofan dakin ahankali, ta karaso gaban gadon da take kwance ga ruwan drip an daura mata, ta zauna kusa da ita ta riko hannun ta , tana mamakin abunda ya firgita hajiya da jininta ya hau sosai, duk sai taji tausayin hajiya ya kamata, batasan lokaci da ta fara zubda hawaye ba , burinta kawai Allah ya sada ta da maihaifiyar ta wataran koda amafarki ne. Digan hawayen da hajiya taji ahannu ta yasa tafara motsi tana kokarin bude ido, ahankali harta bude idonta, ta kalli kursum dake kuka, afirgice ta tashi ta ruko hannun kursum tace “Kursum ashe baki mutu ba” Agigice kursum ta dago ta kalle ta………..:oops::oops::oops::oops: Rudani, tashin hankali, faduwar gaba, lokaci guda ta shiga:oops: *Xarah Bêê* KURSUM By ~ Xarah Bukar page Hankali tashe Tace “hajiya nice sumayya ba kursum ba, amma sam hajiya batasan inda kanta yake ba, ihu sunan kursum kawai take, doctor ne ya shigo dakin da sauri jin ihu ta, ya tsira mata allurar bacci. Ya kalli kursum yace”wace mai sunan da hajiya ke kira? “Tace nima dai doctor bansani ba,ko adangi banji mai sunan ba, “ya nisa yace tabbas mai sunan tana da alaka da shock din da hajiya tashiga, amma karki damu idan ta tashi she will be normal, “tace toh dr mungode, ya fice. Itama taja kujera ta zauna tayi tagumi, tunanin ta daya wace kursum din da hajiya ke ambata, dan tunda take da sumy bata taba mata xance wata kursum ba. Ranta abace ta iso gidan aminiyar ta tana kuka, meerah dake baje afalo daga ita sai bom short da bra ga uban giya agabanta, ” ta ajiye cigarette din hannunta, ta karasao wanjenta dasauri,”tace zee mi aka miki? Miya faru? Kukan mi kike? Zee takara fashewa da kuka tace “girlfriend wai yau ni ya yazid ya mara akan wata shegia yarinya, “meerah ta kwalala ido waje, tace babe gayamin wace yar iska ce yanxu in maki maganinta, “zee ta gyara zama ta zayyane mata komai akan sumy, “meerah tayi kwafa tace lailai galfrnd, akan small brat dinnan duk kika birkeci, yanxu abunda zamuyi shine gobe muje har school din da aka jefar da ita a bauchi mu binciki past dinta, dan na tabbata she will have some dirty secret da take boyewa,” zee tace nima dai I dnt trust her, dole mu samo abunda zamuyi using against her, “meerah ta zuba giya a cup ta mika mata,tace just drink diz banason ganinki haka plz, chill up babe akwai casu anjima, ” ta amsa tayi murmushi, ita dai tana son meerah sosai cox she is always there 4 her. *wace ce meerah* Asali sunanta Amirat oyekola, haifaffiyar garin lagos ce, sun hadu da zee a lagos state university inda department dinsu guda, ganin zee yar masu kudi ce marar wayo yasa ta shishige mata har suka zama best friends, duk wata harka ta shaye shaye da clubbing saida ta koya mata, taso tasa zee a harkar bin maza amma taki yadda. Sun kare degree ta tattara tabiyo zee kano har gidansu, acewarta ta gaji da talaucin iyayenta, “haka tayita harkar kawo samari gidan, daga karshe hajiya ta koreta tabar gidan, wani daga cikin samarinta suka kama mata gidan da take yanxu. *cigaban labari* suna zauna a parlour suna hira “yace umma barin leka huzaifa kwana biu bamu huda ba, tayi murmushi tace a daren nan, gayamin gaskia dai kodai gurin sumy zaka, dannan lura da kallon dakake mata dazu, ya sosa keya, “Allah umma wajen huzaifa zani kuma yarinyan nan babu komai tsakani na da ita,”tace to son saika dawo, “kaima dai yakamata kayi auren, ga abokinka ya dade da aure shiyasa ma ya rage zuwa nan,”yayi dariya yace umma karki damu very soon xanyi, ya fice. Zaune suke suna cin abinci sukaji knocking din kofa,ta tashi da sauri ta zura hijab taje ta bude,”tace ya yazid yau kaine a gidanmu sannanu da zuwa, “yayi dariya yace amarya bakya laifi, ya karasa ciki, huzaifa yace “aina dauka yauma baza ka zoba aiki yama yawa, yazid yace toh gashi nazo kuma dama yunwa nake ji, nazo adaidai, “huzaif yace to ai xama zakayi mu baje, “salma dai dariya kawai take dan tasan basa wasa da abinci. sun gama Ci suka hau hira, huzaifa ya yace “angon zee wai yaushe xamu kawo maka itane, yazid ya bata rai yace “zee ko matsala, banma gayama ba hajiyarsu ba lafiya tana asibiti, huzaifa yace kace suruka dai ba lafiya, “yazid ya kaimai duka yace nifa bance maka zan auri zee ba, “Salma tace gaskia ya yazid zamu biya gobe mu dubota duk da bana shiri da xee, “huzaifa yace kodan darajan amintakar su da umma yakamata muje, “yazid yace to Allah ya kaimu goben, xan biyo sai mu wuce, ya musu sallama dare yayi ya wuce. samira ta kawo masu komai da zasu bukata, wajen 10pm doctor mallik ya shigo dubata, “ta tashi jikin da sauki, ya kalli kursum yace,”data farka ba tace komai ba? “tace eh, ya mika mata magunguna, yace wanna joltan valsartan 160 mg na hawan jini ne, zata na sha sau daya a rana, Aspirin cardio 100mg zai taimaka wajen narkar da jini daya hau kanta shima sau daya zata sha, ku tabbata tasha su, “tace toh Dr nida kaina zanna bata, “yace jikin nata yayi sauki gobe xan sallame ku, “tace Allah kaimu ya fice. tashi tayi ta ninke kayan sallarta ta ejiye gefe, ta karaso gaban hajiya dake Zaune tayi tagumi, “tace hajiya sannu kina bukatan wani abu?? tace taimaka min in watsa ruwa kawai. “ta rike hajiya har toilet ta watsa ruwa tayi alwala ta fito tafara sallolin.. *washe gari* Duk sun hallara a asibiti umma na zaune kusa da hajiya suna xantawa kasa kasa, kursum na gefe tana hada musu kayansu waje daya, shi kuwa oga yazid ya kame kan kujera yana waya ya zuba mata idanu,”da sauri ya tashi yace umma barin je in shigo dasu huzaifa suna waje” tace to my son,” ta kalli hajiya tace bakwa hira da sumy ne ?? naga tunda mukazo tana gefe tayi shuru, hajiya taya tsine fuska tace “ina ruwana da ita” umma tace haba hadiza tunda kin rasa yarki Ai ya kamata kija sumy ajiki tamkar ke kika haifeta, tsaki hajiya tayi tace nifa banason ta, xan jata ajiki kawai dan inji labari kursum daga bakinta. yazid ya shigo tare da huzaifa da salma, suka gaishe da umma da hajiya, umma tace angama amarcin kenan tana zolayan salma amarya, huzaifa yana dariya yace kakus (sunan dayake Kiran hajiya) an tabo file kenan, ya jiki ? hajiya ta harare shi ta tace” nagaya ma ban tsufa ba har yanxu am 16 kana cemin kakus, gaba dayan su saida suka dara, sai sannan suka lura da kursum dake dariya daga gefe, huzaifa ya kalleta yace yammata daga ina ? tayi banza dashi, “yace umma ina kuka samo yarinya mai kama da kakus, yazid yayi caraf yace ai yarta ce, zai sake magana hajiya ta wullo mai harara, ba shiri yayi shuru, “salma tace nikam nasamu kawa, takarasa wajen kursum, tace kawata bakya magana ne? kursum tayi murmushi tace “inayi mana yakike ? ni sunana sumayya, “salma tace gaskia naji dadi saninki dama banda kowa agarin nan, kursum tace u are welcm nima am happy to meet u. ………huzaifa na gefe yana waya, yazid ya karaso wajen su ya zauna, ya kashewa kursum ido yace “my witch anyi sabuwar kawa an manta dani koh ?? ta bata rai ta murguda baki tace ina ruwana dakai, u are my enemy not a friend, yayi dariya yace bakisan enemies na zama best frnds ba, “salma dai bunsu tayi da Ido, “huzaifa ya gama yace”umma nizan wuce ana naima na a office, tace to son kayi kokari ma, ya kalli hajiya yace kakus get well soon, “salma ki zauna tare da kawarki later zanzo in dauke ki, tace toh , yabi kursum da kallo ya fice, yazid daya lura da abokin shi, yatashi fuska a daure yace umma sallaman sai yaushe ne? nafara gajiya da zaman asibiti, “hajiya tayi caraf tace kaga yaro da rigima, ai tunda bagaka zee ba dole ka damemu, idan ka gaji kaje waje ka zauna mana, “a fusace ya fice yayi waje dan yasan halin hajiya, “umma tace kwantar da hankalin ki, keda baki da lafiya miye na tada jijiyar wuya, ” kursum dake jinsu bata ji dadin abunda hajiya tace ba, kaman ta fita ta bishi amma ba dama… Baba shehu ne ya shigo da takardar sallaman hajiya, yace su zo su wuce ya sauke su gida, kursum da salma suka kwashi kaya, umma ta taimakawa hajiya ta mike suka fice, “yana zaune cikin mota, umma tashigo tace muje koh, yace su hajiya fa ? tace suna motan shehu, muje gidan “yace toh umma. sun iso gidan, samira ta fito da sauri ta gaishe su ta kwashi kaya tayi ciki dasu, kursum da salma suka shigar da hajiya, baba shehu ya juya ya koma office. “umma tace son bazaka shiga gidan bane, “yace umma barin jiraki anan kawai banason shiga ga mitar hajiya ga kuma zee da rigima nasan tana ciki, “tayi dariya tace yau kuma zee ake boyewa, to barin shiga agurguje in fito, ta wuce shi kuma ya karasa garden ya zauna. ……. Sauri suke ta karaso gida ta canxa kaya su wuce bauchi , tun sassafe su kayi niyya tafiya, till dawn party din da sukayi yasa su bacci har rana, meerah tace galfrnd kiyi parking a waje kawai ki shiga ki canxa kaya ki fito mu wuce kar muyi dare, ” zee tace karki damu babe bazan jima ma,” meerah tace yauwa karki manta da kudaden dazaki kwaso, tace toh hajiya da umma na sama adaki suna xantawa, kursum da salma suna parlour suna hira, “samira ta sauko tace antee sumy umma na Kiran ki, kursum ta tashi da sauri ta haura sama, ta shiga dakin da sallamanta, umma ta amsa da fara’arta tace yauwa sumy yayanku na waje ki kaimai ruwa yasha,”tace toh ta fice, taje kitchen ta dauko bottle water ta fita haraban gidan, can ta hango shi shinkide kan kujera, ta karaso, “idon shi rufe da alama bacci yake, tayi murmushin mugunta ta bude roban ruwa zata tsiyaya mai a fuska, “karaf taji ya rike mata hannu gam saida ta tsorata, ya mike tsaye yana kallonta,”tayi karfin halin cewa miye haka na rikemin hannu, yace ai yau bazan sake kiba saikin gayamin dalilin dayasa kike cemin am ur enemy, “tayi shuru batace komai ba. Agurguje tayi parking awaje, ta shigo gidan da saurin ta, gabanta saida ya fadi hangosu tare rike da hannu ta, wani irin bakin ciki ya mamaye zuciyan ta, wato yarinyan nan bazata fita harkar saurayina ba, lailai kuwa I have to destroy her once n 4 all, ta karasa parlour da sauri dan karsu ganta, bata ankara ba taji salma tace “zee daga ina haka ? saurin mi kike ?? “ta juyo a fusace tace I don’t owe u any explanation, dan kina matar abokin yazid dat doesn’t give u d right to interfere in my life, taja uban tsaki ta wuce, salma kam bataji haushi ba, tasa ba da cin mutuncin ta, dan farkon haduwan suma ce mata tayi she is 2 local tayi harka da ita. hmm ko dakin hajiya bata shiga ba ta wuce dakin baba shehu ta kwashi kudade masu yawa da papers na address din makarantar sumy, ta wuce dakinta tasa wasu matsatsun english wears marasa mutunci, ta sauko koh kallon salma batai ba ta fice, “salma tace Allah ya shirya, gaskia dai ya yazid baiyi saan mace ba. koda ta fito suna nan tare, saidai yanxu zaune suke da alama hira suke, tayi kwafa ta wuce waje, taja mota sai bauchi, meerah na magana ko kollanta batai ba, sharara gudu kawai take. kinyi shuru baki ce komai ba, tace to ya yazid me kakeso ince, nidai kawai I don’t like u datx all, yayi dariya yace karya kike nasan kina sona, ta bata rai ta tashi zata tafi, yace my witch karki tafi zauna in baki labarin rayuwata, “ta kara tamke fuska ta zauna tace ina jinka, “yace kinsan dai no one is perfect koh ? ta girgiza kai alaman eh ,”yace ni nan da kike ganina nayi making alot of mistakes arayuwana wanda har yau am still regretting, “akwai wata yarinya dukda na manta sunanta, but I will never forget her smiling face, ya gyara zama zai cigaba da magana umma ta fito tace mai su tafi , ya tashi ya killi kursum yace next time idan mun hadu zan karasa miki, “jikinta a sanyaye ta bishi da ido tace toh, ya wuce, tayi shiru tana tunanin, wato ya yazid bai manta da sumy ba, amma meyasa bai dawo gareta ba ko sau daya ba ?? jiki ba kwari ta shiga ciki, salma tace ke kuwa daga kai ruwa kin makale, kursum tace aiko ban dade ba, “muje dakina muyi hira zaman parlour ya isheni, suka wuce daki, salma ta dale gado tace “anya sumy ya yazid ba sonki yake ba, “kursum tace haba dai, aini ko sona yake bazan yadda ba, saboda he is really good at playing women’s heart, “salma ta kwalalo ido tace dama kinsan shine ,”da sauri tace a’a, salma tace au nayi mamaki ne, dan ya huzaifa ya taba gayamin ya yaudari mata ba kadan ba amma yanxu kam ya daina, mata basa gabanshi.”kursum ta sauke ajiyan zuciyan, aranta tace Allah yasa dagaske ya shiryu. Sun iso bauchi around 6pm direct makarantar suka wuce, suna zuwa har office din gimbiya Hafsatu aka gaisu, gimbiya na zaune rai abace sai hada tarkacen ta take waje daya, suka shigo da fara’arsu suka ja kujera suka zauna, ta kalle su tace kuna bukatan wani abune yan mata ? zee tayi shiru, meerah tace mu yan garin nan ne, dama cigiyar kawarmu muke, munaso kidan bamu details akanta na zamanta a makarantar nan. gimbiya ta nisa tace miye sunanta ? zee tace sumayya tanimu bawa, “gimbiya ta kare masu kallo aranta tace karya suke, dan sumy bata da wasu frnds sai kursum, kuma daga gani yan bariki ne, kila sunji labarin dukiyar da ubanta ya mutu ya bar mata shiyasa suke naiman ta suci arziki, toh Basu isa ba nice xanci arzikin nan. Tace yammata sai dai kuyi hakuri record dinmu confidential ne bama fitar dashi, “zee zata fara roko meerah ta tabo ta tayi shuru, meerah ta bude jakar xee ta fiddo da makudan kudi ta tura su gaban gimbiya tace ko nawa kike so zamu kara miki ki gayamana abu akanta kawai, “gimbiya tace lailai yau na hadu dayan duniya, ta masu kallon banxa tace ku fice mun daga office kafin insa ayi waje daku, Meerah tace toh xamu tafi, ta dauki paper ta rubuta mata contact dinsu incase in ta canxa mind din gayamasu wani abu, suka fice. gimbiya taja tsaki ta dauki paper tasa a dust bin, ta kwashe kudin tasa a jakar ta, “dama naiman kudi take ido rufe, saboda gwamnati tayi seizing licences dinta na makarantar akan zarginta da ake na saida dalibai,” tayi murmushi tace sumy amfanin ki yazo rayuwata, ta binciko file din sumy ta kwashe address din gidan su…….ta kyalkyale da dariya tace gobe sai Kanon Dabo :oops::oops::oops::oops:Hmmm tashin Hankali kursum get ready gimbiya na hanya. *Xarah Bêê* *Dedicated to bady social* ~Luv u all~ [05/09 12:52 pm] xarah bukar : KURSUM By ~Xarah Bukar Page Da daddare huzaifa yazo daukan salma, har bakin mota kursum ta rokata,suna ta hira da dariya kaman dama sunsan juna”ta gaida shi ya amsa da fara’a sa yana tsokanar ta da autar kakus (hajiya),tayi dariya tamasu sallama ta koma ciki…….. Bayan kwana biyu jikin hajiya yayi sauki, “kursum ta shigo dakin rike da magani da ruwa, tace hajiya lokacin shan magani yayi “ta ya mutse fuska tace maganin sai dacin tsiya a dole kawai nake sha, tayi murmushi ta zauna tabata maganin da ruwa tasha sannan ta gyara mata kwanciya, zata fita hajiya tace Sumy kawarki da kukayi accident, ta rasu iyayanta sun sani kuwa? Dam gaban kursum ya fadi, ta dawo ta zaune tace Ai marainiya ce bata da kowa, dama gidannan zamu zo, “jikin hajiya yayi sanyi,da gangan dama ta tambaye ta Dan taji labarin yar’ta ,ta nisa tace Allah yaji kanta amma ya akai tayi surviving a skull din tunda kince bata da kowa “kursum dake sharar kwalla tace abun tausayi ko kayan sawa gimbiya bata siyamata saidai Sumy ta bata akayanta,excursion ma baa zuwa da ita,tunda bata da kudin biya,” hajiya tace wace Sumy CE ke bata kaya? Kursum data gano kuskuren magananta tace ni mana Nike bata kayan. Ran hajiya ya gama baci, aranta tace wato diamonds din da akaba gimbiya cinyesu tayi,alhalin ko wana diamond worth 2.5 million ne ,shine ko kayan sawa bata iya siyawa yar’ta, wani irin tsanar gimbiya taji……”ta kalli kursum tace ke tashi ki ficemin daga daki ,”kursum tace daga hira kuma sai kora kaman nayi laifi ,ta tashi sum sum ta fice, tana mamakin halin hajiya wataran ayi hirar arziki wata ran kuwa ba mutunci… Kina ganin akwai Hope kuwa,kwana biyu da dawowan mu amma shuru matan nan bata Kira ba, “meerah tace haba zee duk kin tada hankalin ki, idan ma bata kira ba zamu samo wani mafita, zee tace ai dole in damu dan yanda nake ganin taketaken ya yazid zai iya rabuwa dani ya komawa Sumy, meerah taja tsaki tace karfa ki manta tun farko dama baice yana sonki ba,kece kika makale mai, so don’t be surprise idan ya rabu dake, zee ta bata rai tace koda na makale mai aiya kulani, kuma yanxu Gidan su zani coz nasan he is still angry with me ko calls dina bai picking ,ko kallon meerah batai ba ta suri Jakarta ta fice……… Zaune suke a dinning suna lunch, Umma tace “son hurry up ka wuce airport saura 1hour flight din abbanka yayi landing, banaso ya jiraka, “yace toh umma ina gamawa xan wuce,” bugun kofa sukaji anayi da karfi, umma ta kwallawa hajara (mai aiki) kira taje ta bude,”tana budewa zee ta ban gajeta ta shigo ciki tana kwalla wa ya yazid kira batama lura dasu ba, umma ta bata rai, azuciyan ta tace dama nasan sai crazy girl dinnan, dan haushi fasa cin abinci tayi ta tashi zata wuce, “yazid yace umma baki ci komai ba ? Tayi banxa dashi, sai sannan zee ta lura dasu,ta karaso da sauri tace baby ashe kana nan shine kayi shuru,ta kalli umma tace sannu,” umma ta balla mata harara ta wuce. Taja kujera ta zauna ta tace “baby miyasa mom dinka ke treating dina lyk nobody kaman ba future in-law taba, “ya tamke fuska yace” Ai baki taba gaishe taba iyaka cinki sannu, sannu ko ba gaisuwa bace, ta turo baki tace “nifa ko babana bana gaisarwa balle ita, bata isa ba, yazid daya gama fusata ya mike tsaya yace uwartawa CE bata isa ba ? hankali kwance tace Yes, ” Rai abace yace ban taba sani u are crazy ba saiyau ya dauki car keys zai fice, tayi saurin riko hannun shi ta rungumo shi ta baya tace yes am crazing in love with you, “a fusace ya tureta,ya kalle ta yace diz is not love,u are only obsessed with me, infact nida ke it over……what ta fada a firgice tace are u breaking up wit me? Yace yes,ko juyowa baiba ya fice abunshi. Duniyar gaba daya tai mata zafi, kuka take rusawa ta shiga fasa plate da cups dake kan dinning ,tabbas tasan saboda Sumy ya rabu da ita,amma tayi alkawarin bazai taba samun taba cox sai tayi destroying life dinta, sai zage zage take kaman tababbiya. Umma dake daki ta fito da sauri jin fashe fashen yayi yawa, ganin zee na displaying madness yasa ta kira hajara tayi waje da ita…..zee tace basai anyi waje dani ba, nasan hanya, kuma nasan makircin kine yasa ya yazid ya rabu dani, “Allah ya shiryeki kawai umma ta iya ce mata, taja tsaki tabar gidan. Office din baba Shehu ta wuce, yana zaune yana waya ta banko kofa ta shigo tana kuka, ba shiri ya ajiye wayan ya karaso gabanta yace zainab kukan mi kike ? Ina kika shiga kwana biyu ban ganki ba ?” Cikin kuka ta tsara mai komai har zuwan su bauchi, baba Shehu yayi dariya yace halina dake u ar alwyz crazing bakya Abu da tunani, “ta bata rai tace Baba ka daina cemin am crazing ina da hankali, I don’t knw y mutane ke cemin banda hankali, yayi shuru yana tunani, koda ya auri jamila (maman zee) tana da mental illness harta rasu, shiyasa sumtymz zee take abu kaman mai hauka, ya nisa yace ,” am sorry auta ta….ta kyalkyale da dariya tace to baba yanxu miye mafita, yace karki damu zan tura private detective dazai binciko miki komai akan ta, tun daga ranar da aka kaita school din, abunda kikeso kenan koh ?da fara’arta tace eh, yace toh yanxu abu biu zakiyi idan kinaso komai ya tafi daidai, da sauri tace me ? Yace dole ki nunawa yazid kin hakura dashi sannan kuma kija Sumy ajiki yadda bazata gane abunda kike shirin yiba, ta kwalalo ido waje tace”gaskia baba bazan iya, yace toh ke kikasani tashi ki tafi,”ta ma rairace fuska tace na yadda xanyi, yace toh ki wuce gidan kafin in zo tace OK ta fice da murnan ta…… Shima sai murmushi yake dan perfect tym yake jira ya kawar da Sumy once n 4 all. Washe gari, hajiya na zaune a parlour tana cin abinci, zee na kallon TV, kursum ta sauko zata wuce office kusan kwana biu bata jeba, ta gaishe da hajiya ,”ta amsa a yatsine ne ,zee dake gefe tace my sis har zaki tafi,kursum da taji maganan bambarakwai,tace eh ta masu sallama ta fice. Zata shiga mota taji hayaniya abakin gate, ta karasa wajan da sauri, mai gadi daya hango tana zuwa, ya kalli matar dake tsaye da Da niki nikin akwatuna, yace yauwa ga madam Sumy nan zuwa kwayi magana dan bazan bari ki shiga gidan nan ba,”gimbiya tayi shewa tace gidan nan shiga daram. Tana leka waje sukayi ido hudu da gimbiya hafsatu,dam gabanta ya fadi ,gimbiya data gama tsorata tace baki mutu ba dama…….. Da sauri kursum taja ta gefe ta tace mi ya kawo ki gidan nan, gimbiya tace aike xan tambaya kin mutu miya kawoki nan,INA Sumy ? Kursum tace ai Sumy CE ta rasu bani ba, yanxu haka yan gidan sun dauka nice Sumy, long story ne idan mun zauna xan baki labari ,”ta bude Jakarta ta zaro makudan kudi ta mikawa gimbiya tace ga wannan ki koma bauchi yanxu nan, zamuyi waya……gimbiya ta kece da dariya tace Ai baki isa ba, babu inda zani, kursum tace koki tafi ko in kira securities su fitar dake daga nan, “ta kara kecewa da dariya tace ai ke zabi ya ragewa, ko ki barni in zauna a gidan ko kuma inje in tona miki asiri,kinga dagani harke mun rasa , balle ke da baki da wajan zuwa. Kursum data gama kulewa tace Baza ki zauna a gidan ba, kiyi abunda zakiyi. Gimbiya tace toh zakiga Abunda zanyi kuwa, ta bangaje maigadi ta shige gidan da gudunta, Agigice kursum ta bita tana cewa tsaya!! Tsaya!! Muyi magana, amma ina…..gimbiya tayi nisa batajin kira, harta karaso bankin parlour ta tura kofa ta shiga…….. Tashin sense :oops::oops: *Xarah Bukar* *Dedicated to Bady social* ~Luv u all~ kursum 56 to 58 Posted by XARAH ABUBAKAR on NOVEMBER 13, 2016 [06/09 10:53 AM] Xarah Bukar : KURSUM by ~ Xarah Bukar Page Hankali kwance ta tura kofan ta shiga da sallaman ta, hajiya ta amsa tace waye ? Zee ta juya taga gimbiya, tace baiwar Allah aida baki zoba kin kiramu ta waya, sai sannan gimbiya ta gane zee, itace marar kunyan nan da sukazo naiman labarin sumy, taja tsaki tace bansanki ba kuma ba wajan ki nazo ba, hajiya tace zee kinsanta tane ? Zee tayi shuru, hajiya tace bakuwa gurunwa kikazo ? Caraf kursum ta shigo tace gurina tazo, kuma a gidan nan zata zauna, hajiya tace bazata zauna ba, Ai nan ba hotel bane daza ki kawota, gimbiya tace haba hajiya nice fa gimbiya makarantar da Sumy tayi harta girma, yadda na kulan miki da ita bai kamata ki Kore niba, “ran hajiya ya gama bacci, wani irin tsanar gimbiya taji a zuciyar ta,aranta tace wato matar nan itace ta maida min kursum abun tausayi ko kaya bata siya mata. Ta nisa tace koda kike riketa aiba kyauta bane kudi aka baki, na baki minti biyar ki ficemin daga gida….. Gimbiya ta kalli kursum tamata signal kotasa baki ko kuma ta tona, ” kursum tayi Gyaran murya tace gaskia hajiya saidai kiyi hakuri, dole gimbiya ta zauna agidan nan, tunda gidana ne, “hajiya data gama fusata tace to na yadda ta zauna amma ba nan tare damu ba, ki kaita can bangaran masu aiki ta zauna, kursum zata kara magana hajiya ta daka mata hannu tace nagama magana, ta dogara Sandar ta tahau ra sama…….kursum tace nizan wuce office ta fice,da sauri gimbiya tabi ta tace amma dai hajiyar nan bata da mutunci, kursum tace karki CE haka dan kuwa bata da matsala, kiyi hakuri ki zauna a part din masu aiki kafin insamo mafita, idan kika Kama kanki zakiji dadin zama da ita, makauniya ce ba gani take ba,gimbiya tace kina nufin duk kwalliyan datayi da uban dauri da bakin glass din bata gani ? Tace kwarai kuwa,tun wajan shekaru 18 da suka wuce tasamu matsalan ido, gimbiya tace shikenan ki tura masu aikin su gyaramin dakin, kursum tace toh kayan ki ma xansa ashigo dasu, xan wuce aiki saina dawo. Gimbiya ta koma parlour ta zauna, zee ta kalle ta taja tsaki tace ashe bakin ku Da ita shiyasa kika ki bamu details akanta, gimbaya tace yarinya ni kike jawa tsaki ? Zee tace eh mana ke wace CE ? Gimbiya ta mike taje har gabanta ta kama mata kunne gam tace idan kina takama ke yar bariki toh ni sunana na biyu bariki, ki kiyaye ni danni ba tsarar wasanki bace,kina jina ? Zafin da taji yasa Ba shiri tace eh naji kisake mun kunne, saida taga kunnen yayi jajir sannan ta saki ta koma kan kujera ta baje, “da sauri zee ta tashi tace muguwa ta gudu sama……….. Agurguje plz…….. Kursum ta koma bakin aiki, takan kiran inna taji ya hanifa, tsakanin ta da yazid sai wasa buya bata barin su hadu dan ta tabbatar ta kamu da son shi. tsoranta daya bai wuce kar asirinta ya tonu ba. Hajiya ta warware sosai, bata shiga harkan kowa a gidan kullum tana makale adaki, kursum tana shigowa gaisheta ta bata magani. Yazid ya kanzo gidan ganin kursum, amma sai dai yasha zama a parlour bata fitowa, idan yagaji ya tafi…. Zee kuwa basu da aiki ita da meerah sai clubbing da shaye shaye, takan yi kwana biu bata kwana gida ba, ta fita harkan yazid ko sun hadu bata kulashi, dukda sonshi na nan daram azuciyar ta, har dakin kursum take shiga tayi ta janta da hira kaman gaske. Baba Shehu na nan da kudirin sa, burinsa ya kawar da Sumy,amma ya rasa yazeyi. Gimbiya hafsatu ko yaushe tana main house abaje a parlour bata da aiki sai tsegumi, kowa haushin ta yake ji agidan, tunda taga Baba Shehu take shishige mai, ita adole tasamu mijin aure, shi ko kallon bata ishe shi ba….. Bayan sati biyu Umma ce taxo gidan tayi knocking kofa, gimbiya dake kallon TV taja tsaki ta tashi taje budewa, ta bude suka gaisa da umma, umma tace amma ke bakuwa ce koh? gimbiya ta Kare mata kallo tace wata sabon gani hajiya maryam ai bazan taba mantawa da fuskan kiba, umma ta kwalalo ido waje tace ina kika sannni nikam bansan kiba……gimbiya ta kece da dariya tace Ai dole kimanta ni, 18 years ago kika kawo min kursum tana jaririya kokin mata ne? Umma ta bata rai tace banganeki bane, me kikeyi a gidan nan ? Tace zama nazoyi mana Ai Sumy daliba tace, umma tace toh yanxu babu komai tsakani na dake, tunda kursum ta rasu, karki kara gani na kice kin sanni, gimbiya tace haba hajiya miya yayi zafi haka, ki bari muyi zumunci mana,” tayi banza da ita ta wuce sama dakin hajiya. Gimbiya tace lailai matan nan,aiko saina juyo xancen da zakuyi, sadaf taje bakin kofan dakin ta kasa kunne… Hajiya tace ashe zaki zo, na dauka kokin mata dani, umma tayi dariya tace yanxu ma agurguje nazo Alhaji na gari Shiyasa kika jini shuru ,ya karfin jiki ? Hajia tace da sauki sosai, Ina son dinki kwana biu baizo ba…….umma tace indai yazid ne anjima kina iya ganin shi, ta duba agogo, nizan wuce office sai munyi waya,”tayi sallama da hajiya ta fice. Gimbiya dake labe ta bar wajan da sauri, aranta tace oh kakkyawan yaron nan dake zuwa wajan kursum ashe danta ne, ta kwalalo ido waje, idan umma ce uwarsa kenan yazid da kursum are siblings basu sani ba, ta koma bakin kofan ta tura ahankali tashi ga dakin, hajiya na zaune kan gado tana kallan pictures din daddy tana sharar kwalla, bata ankara ba sai ganin gimbiya tayi gabanta, arazane tace miya shigo dake nan, gimbiya data cika da mamaki tace keda kike makauniya hw cms kike kallon picxx, hajiya duk ta kideme,da sauri tadau glass dinta ta maida, munafuka fice min daki kafin insa ayi waje dake, “tayi shewa tace ai ina fita xan tara kowa a parlour ingaya masu Karya kike 4 d past 18yrs, kina gani kuru kuru,” afusace hajiya tace Fadi price din da kikeso in baki kiyi shuru da bakinki, gimbiya tace banason kudi idan kikamin abu biyu toh ur secret is safe wit me, tace mai kikeso ? Na farko inaso indawo main house da xama nagaji da zama part din masu aiki, na biyu kisa Shehu ya aure ni, ” hajiya taja tsaki, na yadda dana farkon, amma na biyu I don’t tink zai yuyu, bazan ma kanina auran dole ba,balle ke yar bariki wace tayi aure wajan shida ta kasa zama, gimbiya data gama kulewa tace toh naji ,xan baki time kisan yadda kikai ya aure ni, ta fice afusace kalaman hajiya sun bata haushi. Agajiye ta dawo daga office tayi sallan magrib ta fada gado, ta dauki wayanta taga 10 missed calls da sauri ta tashi zaune ganin number inna sadiya, ta buga ringing daya Inna ta dauka, jin kukan hanifa yasa kursum ta gigice, tace Inna miya sameta ? Kukan mi take? Inna tace wlh zazzabi ke damunta tun jiya munje asibiti amma ba sauki har yanxu shiyasa ma nake kiranki,” hankali tashe kursum tace inna dare yayi balle inzo, Ki cigaba da lallashin ta, gobe da sassafe zanzo in dauke ta, Inna tace toh sai kinzo, sukayi sallama. Tunani take yadda zata dawo da hanifa gidan, bata da wani mafita ,da sauri ta tashi ta sauka kasa, suna kan dinning suna cin abinci ,zee sai wani bata rai take ganin gimbiya zaune dasu tana wurga loma, ta kalli baba Shehu tace waimi matar nan keyi anan ? Hajiya tayi caraf tace ke bana son rashin kunya, kici abinci……..kursum ta karaso ta zauna tace baba xan tafi bauchi gobe, ya kalleta lafiya dai ko ? Tace eh, inaso kasamo mun driver dazai kaini kasan ban kware sosai ba, “zee tace sister y not inkai ki, baba Shehu ya watsa mata harara, bazaki kaita ba, ya kalleta kursum yace karki damu zan shirya miki driver dazai kaiki gobe wajan 8am, tace toh nagode baba, hajiya ni xanyi tafiya gobe xanma doctor malik magana ya turo nurse dazata na baki maganin ki, ” hajiya taja ta tsaki tace shekara zakiyi kenan ? tace a’a agoben xan dawo xanyi dare dai, tace to asauka kalau ta mike ta wuce Daki, Baba shehu ma ya tashi ya fishi, zee data gama kulewa tayi wurgi da glass cup din dake hannuta ta fice daga gidan…..gimbiya ta kalli kursum, amma zainab dinnan is crazy koh ? yauwa mi zaikai ki bauchi? kursum tace hmm hanifa xan dauko bata da lafiya,” gimbiya tace tashin hankali idan kika dauko ta mi zaki cewa masu gidan, yarki zakice ko wa? Tayi banza da ita ta tashi ta wuce…. Wajan karfe dayan dare, tana parlour tana kallon TV, taji motsi kaman ana saukowa kasa, da sauri ta kashe wutan ta labe bayan kujera, taji yana waya “yace bala kajira ni bakin gate gani nan zuwa ya fice waje, gimbiya dake labe tace shehu wazai gani a darannan, sadaf ta bishi ahankali har waje, baba shehu yace bala nasan zaka iya aikin shiyasa na samoka, gobe karfe 8am zakazo ka kaita bauchi, bala yace angama duk yadda kace haka zaai, “yace yauwa ashe ka gane, kasheta zakayi idan kunyi nisa ka jefar da gawar ta yadda babu Wanda zai gani, sannan kai kuma ka bace kabar gari, ya fiddo makudan kudi Ya damka mai, bala ya karba yace angama, sai nazo goben, sukayi sallama ya koma ciki da sauri. Gimbiya dake labe tana jinsu saida ta girgiza, mamaki kawai take kowa da hidden agenda dinshi a gidan, hajiya mai karyan maganta, zee d crazy gal, ga umma da yar’ta amma bata saniba, shehu da nashi makircin, kursum dake using identity din dead Sumy, ta tabbata yazid yana da nashi unknw secret din, Wat a mysterious family. Tayi kwafa ta koma ciki, tunani kawai take yadda zatayi saving kursum in 7hours, cox idan ta bari aka kasheta barin gidan nan yakamata dole. *Xarah Bukar* *Dedicated to Bady social* ~luv u all~ [08/09 12:20 am] Xarah bukar : KURSUM by ~ Xarah Bukar Page Tun 7am ta shirya tama hajiya sallama “ta fito haraban gidan jiran driver. “Gimbiya sai kai komo take a daki tun bayan sallan asubah, ta leka waje ta hango kursum tsaye bakin mota tana jiran bala,” can dabara ta fado mata, da sauri ta fice ta shiga dakin baba shehu ahankali, da alama yana toilet, sadaf ta karasa bakin gadon ta dau wayarshi ta ta binciko contact din bala driver,” ta tura mai msg “` “change of plans kazo by 10am”“` tana turawa tayi deleting ta kashe wayan ta ajiye ta fice da sauri, ta sauke ajiyan zuciya, atleast zata samu tym din samu mafita. “Yana fitowa ya shirya da sauri yadau wayoyin sa ya fice, ” kursum dake tsaya ta karaso ta gaida shi, baba kasan 8am zan wuce, gashi 7.45 har yanxu baizo ba, “yace karki damu bala baya wasa da aikin sa zaizo Yanxun nan, ” toh baba Allah yasa karya bata min tym, sukayi sallama baba shehu ya wuce office, aranshi sai murna yake , yarinya zaman ki yazo karshe a duniya. “Sai leke take ta window ta rasa mafita, ta sauko sum sum ta karasa wajan kursum dake tsaye rai abace, “tace anya bazaki hakura da tafiyan ba naga har 9 yayi driver bai iso ba, ” kursum ta kalleta tace haba gimbiya kinsan hanifa amana tace dole in dauko ta, gashi layin baba shehu off bansan yadda xanyi ba, “gimbiya tayi shuru tama rasa me zatace, fatan ta kawai kar bala yazo dan 30mins ya rage goma ta cika… “Hankali kwance yake driving har ya iso gidan, ya kudiri niyya yau saiya ganta koda zata makale adaki, kusan 3weeks kenan yana bibiyanta…. Suna tsaye yashigo, dukta daburce ganin shi, zata koma ciki da gudu gimbiya ta riketa tsam, Ai babu guduwa da zakiyi in har kinason ganin hanif dole ki rokeshi ya kaiki, kursum ta bata rai banason haka, bakisan banaso in hadu dashi ba, gimbiya tayi shewa, tace ahab ai nasan kina sonshi kina kaiwa kasuwa, taja ta har wajan shi ta bude motan ta turata ciki, ” yazid dake kokarin fitowa daga motan saida ya tsorata,Sam bai lura dasu ba sai ganin gimbiya yayi ta turo ta…. “ya tamke fuska, miya haka ? zaki ji mata ciwo ne ? Ta washe baki tace ai nasan wajan ta kazo, sai ka kaita Inda zata, ta kalli kursum da tayi kicin kicin fuska a murtuke, sai ki gayamai inda zaki ta rufe motan ta koma ciki…… “Yaja mota suka kama hanya, ya kalle ta yayi murmushi, my witch ina zan kaiki ? Kaman tayi banza dashi, sai kuma tace ” bauchi zaka kaini… “Ya kalleta, hop all is well. tayi banza dashi Ya cigaba da sharara gudu, can yace miya sa kike guduna ? “Banason ganin ka ne” Ya murmusa yace Y “i hate yhu” Kinsan I hate lies, nasan u Luv me” I dunno y kike cewa u hate me, gashi ni am deeply inluv wit u kina bani tough time….. “Tace hmmm I don’t biliv, infact I don’t trust yhu. Am serious, u can trust me yace mata. Tayi murmushi, last tym da muka hadu baka karasa min labarin yarinyar nan da kuka hadu a bauchi ba, kace ka manta sunanta, kasan inda take yanxu ??? ” ya sauke ajiyan zuciya, matata CE just 4 a nyt, na aureta da kwana daya nasake ta, wat tace “kana nufin u wia once married n divorced ?? ” eh, dat was d biggest mistake da nayi arayuwata, koda na saketa na tafi nakara komawa in dawo da ita, amma it waz 2 late aka cemin ta sake aure tabar nigeria.. Kursum dake sharar kwalla a boye, aranta tana mamaki waya cemai Sumy ta sake aure, ta nisa tace eyya iyayen ta suka gayama ta sake aure kenan ? “Yace a’a, bata da kowa agarin ma, wani jamilu dana tura naiman aurenta a makarantar su shina turo ya bincikomin ita, koda yaje director din tace mai ai tayi aure bata kasar…. ” ya kalli kursum dake zubda hawaye, ya ciro hankie dinshi ya mika ta, kukan mi kike, “ta karba tace it a pity, umma tasan da faruwar haka ? Yace e tasani na gayama ta komai, tare ma muka so zuwa naiman yarinyar, amma she was so busy, ” I hop duk inda take yanxu zata yafemun. “tace am sure ta yafemaka. Kinsan tane, hw are u sure she has 4given me ? ” nayi guessing ne kawai tace mai….aranta mamakin hali gimbiya take, wato ita tayi karyan cewa sumy tayi aure tabar kasar, wat a cruel woman, aiko tana komawa zata fadi gaskia, inyaso daga ita har gimbayan sabar gidan. “Ta dau wayanta ta kira inna, suka gaisa, ya jikin hanifa ” Inna tace da sauki sosai yanxu bacci ma take, inna nima Ina hanya, tace toh kursum Allah ya kawoki lapia, sai kinzo, sukayi sallama. “Ya kalleta yace wace ce Hanifa ???? Ta fuske tace ya’ta CE, Wat yaja birki da karfi, kina da aure dama ? tace banda shi asali ma ban taba yiba, amma inada Ya’ yar shekara daya, dauko ta xanyi bata da lapia, ” yayi shuru bai ce komai ba, yasan dai she is decent ,hw cms take da Ya’ ba aure, Afusace ya tada mota ya dunga sharara gudu kaman xai tashi sama, ni phatee mai dauko rahoto saida na tsorata, wanga sheka gudu kaman ba gobe:oops::oops: Tana baje a parlour (as usual) tana taunar cingam kaman wata yar gidan mangwaro, zee dake kan dinning tana cin abinci ta ja tsaki tace tsohuwar banza haka zaki kare munafuka, “gimbiya ta nuna ta da yatse, ni kike zagi ? Zee tace kwarai kuwa mayya, ta tashi afusace ta kama zee tana duka, ihu take bazan kara ba ki kyaleni, ba mafita ta dankara mata cizo ba shiri gimbiya ta sake ta, da gudu tabar wajen. ” gimbiya tayi kwafa, shegian yarinya nakusa zama uwarki, ubanki ya shigo hannu na dole ya aureni ko yanaso ko baya so *Xarah Bukar* *Dedicated to Bady social* ~luv u all~ KURSUM by ~ Xarah bukar page Babu wanda yace uffan har suka iso garin bauchi, direct gidan inna sadiya suka zarce, “yayi parking yace karki dade cox bana nyt driving, ” baza ka shigo ku gaisa da inna ba? no need, jux hurry up ki fito mu wuce, xan shiga masallaci Toh kawai tace ta shige gidan. Inna na tsakar gida tana wanki taji sallaman ta, ta amsa tace amma dai kinyi saurin isowa “Kursum tace eh wlh inna ya kuke? lapia lau, taja ta suka shiga daki, hanifa na kwance tana Bacci, yanxu kam xaxxabin ya sauka sosai, saidai bata son cin abinci inji inna ” kursum ta nisa tace ai rashin cin abincin nata nada muna, ina isa gida zan kaita asibiti, “inna tace barin kawo maki naci da sha Kidai barshi wlh, muda muke sauri sallah kadai xanyi in wuce, inna tace irin sauri haka, bara na zubo maki ruwa a buta. “Bayan tayi sallah, sukayi sallama da inna tare da bata makudan kudi ta kula da kanta, tadau hanifa suka fice, inna sai zuba godiya ake. “tsaye yake bakin mota yana waya da umma ” son kace tana da ya’ marar lapia ? Haka dai tace min. Okay don’t bother asking her anytn, irinsu nasan situation dinsu, kuna isowa kano ka kaita asibiti, xanzo insa meku “Yace toh. Hey ka gama wayan can we go ya juyo yaganta zaune cikin mota, wen kika fito ko motsin kin ban jiba ” nayi kusan 10mins anan ai, “yayi murmushi ya shiga mota, ya kalli hanifa dake bacci jinkinta yace ur baby is cute tnx kawai tace, suka Kama hanya Baba shehu zaune a office, ya kalli agogo yasan by diz tym she is already dead, wayashi ya dauka zai kira bala driver, yay mamaki matuka gannin wayan nashi kashe, yasan dai baya kashe waya, da sauri ya kunne ya kira bala, bugu daya ya dauka ” ina fatan dai ka cika aiki? Bala yace wana aiki kuma, naje gidan around 10 wata Mata tacemin ai kace anfasa tafiyan sai gobe, nayi kokarin kiran ka layin kashe “ya tamke fuska, kaida nacema 8am maiya kawo ka 10, kuma wace tacema anfasa tafiyan? bala yace ka turomin msg inxo by 10am, ni bansan matar ba, amma daganin ta yar gari ce. Afusace ya tsinke call din ya dauki car keys dinshi yayi waje, yasan babu tantama gimbiya ce ta ruguza mai plans dinshi, amma hw cms tasan komai, lailai ko sai ya koya mata hankali. Tana zaune kan dinning ta hada varieties of abinci sai wurga loma take, ya banko kofa ya shigo, saida ta tsorata ta mike tsaya, shehu lapia ? Ko sauraron ta bai yiba, ya cafko wuyan ta ya shake, bana hanaki shiga tsabga taba ” gimbiya dake kakarin shedewa tace kashe ni zakayi kenan kaman yadda ka tura akasheta, ” ba shiri ya tsake ta ya wurga mata harara, bangane me kike nufi ba tayi shewa, shehu karka raina min yawo, ta fito da wayatan ta kunna mai zancen su da tayi recording, “yayi tsuru tsuru, toh mai zakiyi dashi? “ta kece da dariya, police station zan kai yanxu kuwa, ” haba hafsatu mi yayi zafi haka kiyi hakuri mana….ta balla mai harara, aurena ko prison sai ka zabi daya “Ya kwalalo ido waje, are u trying to blackmail me. za tayi magana hajiya ta sauko, lafiya nake jin hayaniya? gimbiya tayi caraf tace ba komai dama zancen auran mu muke da shehu, ta kalle shi koh shehu ? ” yayi banza da ita ya wuce abunshi. Ta kalli hajiya,nagama part dina sai ki san yadda zakiyi ayi auran cikin sati daya, “hajiya ta balla mata harara, matsiya ciya ai dama nasan zuwanki ba alheri bane, ” ta washe baki, karfa ki zageni kinsan nasan komai, “takaici duk ya isheta tama rasa mizata ce. Karfe takwas na dare suka iso kano, suka wuce asibiti, ” Dr aesherh dangusau ce on duty, da sauri ta tarbesu sanin tasan dazuwan su, suna zaune a office dinta ta gama duba hanifa ta kalle su, babyn ba wani serious sickness take ba, dou rashin appetite ke hana ta cin abinci, ta dau pen da paper, “ta mata prescribing paracetamol syrup na pain relieve, da Oral rehydration salt na restoring body fluid & electrolytes lost due to dehydration, idan tasha zataji dama sosai tace ” ta mika mai paper ya karba tace baby dinnan sam bata kama da mamanta, kamar ku da ita yayi yawa, “nan gaban kursum ya buga, sai yanxu ta kara tabbatar wa da kaman yayi yawa” shiko yazid ko acikin shi, dan baiga kaman komai ba. Suka fito zuwa pharmacy sukayi kicibis da umma ta shigo, “kursum tayi murmushi ta gaida ta aladabce, ta amsa da fara’arta ta amshi hanifa, ” yazid yace umma barin barku anan inje amso magani, tace OK. Taja ta suka samu guri suka zauna, ta kalle kursum tace sumy kinsan na dauke ki tamkar nina haifeki, “yazid ya gayamin komai yanxu gayamin waye uban hanifa ? tayi narai narai da ido, aranta tace danki ne ubanta……..afili tarasa mi zatace kawai ta fashe da kuka, ” jikin umma yayi sanyi matuka, kar kiyi kuka kinji, am sure kina da kamun kai, saidai ko u are a victim of rape.. “kursum tayi shuru batace komai ba illa sharar kwalla da take, “umma tace kirki damu haka Allah ya kaddara, so if u nid any1 to talk to kina iya xuwa kisame ni, kinji ? ” toh umma nagode sosai da kulawarki, aranta tace da umma ce mahaifiyar ta da nayi sa’ar uwa.” ya dawo rike da maganin, ya amshi hanifa yace muje koh suka mike zasu wuce umma taja shi gefe, my son plz karka ce xaka rabu sumy, yanxu yakamta mu taimake ta, kasan yan gidansu ba sonta suke ba, ‘karki damu umma no matter wat ina tare da ita, I will 4ever luv her till eternity. tayi murmushi, tnx my son, tayi sallama da kursum ta wuce gida. shima yaja mota suka bar asibiti. tana zaune a parlour nurse ta shigo tace hajiya lokacin shan magani yayi, “ta yatsine fuska ke nifa karki takura ni da magani, da safe ma nasha. nurse tace kiyi hakuri, aiki na in kula da lafiyar ki, idan baki sha ba abakin aiki na, zee dake kallon tv taja tsaki ta mike, kun cika min kunne da surutu, “hajiya tace baa dole saiki tafi daki kiyi kallo. “turo wan kofan ne yasata tsayawa chak, ganin su tare ga kursum rike da yarinya, ta bata rai, ku kuma da ga ina adaran nan ? ko kallanta basuyi ba suka karasa wajan hajiya suka gaida ta, “ta amsa ayatsine ganinsu da yar yarinya da bazata wuce 1year ba, aranta tace Allah kadai yasan ina suka samota, “tayi gyaran murya, ina jin motsin yara, yazid kazo da baby ne ?? “kursum tayi caraf tace eh ya’ta dama ita naje dauko wa a bauchi. Daga zee har hajiya sai da suka tsorata, lokaci guda suka ce badai shegiya bace. tayi banza dasu, yazid yace ba shegiya bace zee data gama kulewa tace kaine ubanta kenan “yace bani bane amma daga yau nazama ubanta. hajiya tace zainab kiramin gimbiya in ji daga bakinta, dan bazan yadda da shegia agidan nan ba…… Dam gaban kursum ya buga, Allah yasa kar gimbiya ta kufsa mata…. *Xarah Bukar* *Dedicated to Bady Social* ~luv u all~ kursum 59 to 63 Posted by XARAH ABUBAKAR on NOVEMBER 13, 2016 KURSUM by ~ Xarah Bukar Page Hankali kwance ta shigo palon, ganin kursum rike da hanifa yasa tasha jinin cikinta, aranta tace oooh family drama dinsu baya karewa. “hajiya lafia kika naima na ? Ta wurga mata harara, gayamin zakiyi ya akai sumy tayi ciki harta haihu bani da labari ? ” gimbiya ta kwashe da dariya, abu mai sauki ai ita zaki tambaya bani ba, “zee tayi caraf tace dama bakin ku daya, kun gama karuwanci ku tare ai dole ki rufa mata asiri, Hajiya ta daka mata tsawa, ke banson hauka anan, tunda sunki magana kawai tadau shegiar yar’ta ta maida ta inda ta dauko ta. “Yazid da takaici ya ishe shi yace babu inda xata , infact aurenta xanyi sai inga mai ce wa yar’mu shegia, ” daga kursum har zee saida suka girgiza jin kalaman sa Xee ta fashe ihu, baby akan karuwa zaka gujeni, toh wlh baka isaba, ke kuma kin gama iskanci a duniya shine zaki lake mai dan matsiyaciyar yarki tasamu uba ,”kursum data gama fusata ta nunata da yatsa, kince min karuwa nayi shuru, don’t u dare insult my daughter…. “zee ta yi kwafa tace na zaga din shegia, du your worst….tass din kakkyawa marin da taji a kuncin ta yasa ta mut lokaci daya, ” ya wurga mata harara, kara zakinta kiga abunda zan miki, marar hankali kawai, yaja hannun kursum suka hau sama. Zee dake hawaye ta kalli hajiya tace ki taimaka kar ya aureta yabar ni , “hajiya taja tsaki, indai zai aureta aina ji dadi, barinta gidan nan shine farin cikina, gimbiya tayi shewa, buki bidiri aure biyu zaai kenan, ” akule zee ta kalleta, ke kuma yar bariki wazai kwashe ki ? “tayi fari da ido, ashe baki da labari toh ubanki ne zai kwashe ni, aure nan da kwana uku, ” haushi da takaici ya hana ta magana, ta suri Jakarta ta fice daga gidan. Har dakinta ya shigo da ita, ta kwantar da hanifa, ta kifa kai kan gado tana zubda hawaye, “yana tsaye yana kallonta, tausayi da tsananin sonta yaci gaba da ratsa shi, ya yarfe hannuwa gami da durkusawa a gabanta, ” kukan nan naki na breaking heart dina, atleast say sumtim ko zanji dadi. “Ta dago idonta da ya sauya launi tana dubansa, ta kwantar da kai tace ya yazid I don’t deserve ur love saboda ni ba wace kake tunani bace, ” yayi murmushi, ai nasan u wia adopted, hajiya ba mom dinki, kar kiyi tunanin kozan ki’ke dan baki da asali, “ta kalleshi da mamaki, aranta tace nikam ba haka nake nufi ba, inason gayama wace ce ni amma ina tsoron karka gujeni, ” afili ta nisa tace yaya just go I need some space, ya kalleta okay I’ll but promise me u won’t cry again, “tace yes I promise “ok gud nyt ” ya sauko yama hajiya sai da safe ya fice daga gidan. gimbiya tayi murmushi mugunta, yanxu inta auri shehu tazama queen of d house, shiyasa baza ta gayawa kursum cewa yazid yayanta ne ba, gwanda ta aure shi tabar mata gidan….hmm( wa’iyazubillah gimbiya kiji tsoron Allah, dukda munsan basu hada jiniba bai kamata kice haka ba ). ************************ Tana bacci taji an daka mata duka, firgigit ta tashi tana murtsuka ido,”miye haka zaki dakeni? “Meerah tace nayi mamakin ganin kine, yaushe kika zo ? Zee ta gyara kwanciya, ke nifa jiya da daddare na shigo, tension yamin yawa datx y nazo ke kuma as usual bakya nan, Meerah ta kwalalo ido, galfrnd wana tension, gayamin miya Sameki, “humm ta nisa, ta fyade mata biri har wutsiya ” meerah tace anya cousin sis dinki ba jazz tama ya yazid ba, ta gama yawon duniya harda shegia gareta but still he is willing 2 marry her, “zee tace babu wani jazz, dama yana dason yara, ni yanxu bansan ya xanyi ba, ga p.D yace mu bashi nan da sati biu, ” meerah tace karki damu muna da hope ai nasan detective zai samo komai akanta, ita kuma gimbiya ki shareta naga alama matar ba mutunci. “aiko dai, ni bansan hw cms baba ya yadda da aurenta ba, koda yake datz his problem not mine. Abba yayi doguwa ajiyar zuciya ya kalli umma yace narasa miyasa kike son yazid ya aure yarinyan nan alhalin kuma har ciki shege tayi, ” ta bata rai, haba alhaji karka ce haka, kowa arayuwa yana da nasa laifin dan ya aureta aiba haram bane, “ya nisa yace toh shi kenan xanje wajan shehu naima mai auranta, amma kisani duk abunda ya faru nan gaba babu ruwana, ” umma tayi murmushi, babu abunda zai faru sai alheri, yace toh nidai nagama magana, yadau hulansa ya fice. Tun daga wannan ranar wata irin soyayya suke gudanarwa mai cike da kauna, wani lokaci abin yakan baiwa kursum mamaki, shin dama zuciya takan iya son abunda ta tsana da fari ,domin ko taki ko taso ayanxu tasan dan zaman da tayi da yazid takamu da sonshi, dan ba karamin kula da hanifa yake ba…… Salma ce tazo gidan, suka gaisa da samira dake rike da hanifa, “samira Ina kike samu pretty gal ? ” tayi dariya tace ai diyar Antee sumy ce, “salma data cika da mamaki tace sumy na daki ? Tace eh tana nan. ” ta shigo dakin, kursum dake zauna tana shafa mai tayi dariya, kawata yanxu nake shirin calling dinki, salma tayi yake, nima kasuwa zani shine nabiyo, yau baki je office ba, “eh kwana biu bana zuwa, dayake ya’ta bata jin dadi. Salma tace wai dagaske yar’ kice , nidai ban yadda ba, sam baku kama, ” kursum ta sauke ajiyan zuciya, ta tashi ta rufe kofan dakin da mukulli, taja hannu salma suka zauna kan gado, tace kawata yau xan gayamaki sirrin rayuwata, ta tsara mata komai tun daga ranar da mahaifiyar ta tayar da ita har izuwa yau, “ba karamin tausaya mata tai ba tace Allah yaji kan sumy, ni aganina it better ki gayawa yazid gaskia yasan cewa shine uban hanifa, ” kursum ta nisa, inason gayamai ina tsoro karya gujeni, “salma tace karki ji tsoro, ba karamin sonki yake ba am sure he will understand idan kika gayamai, tace toh I will try idan nasamu chance, ” wana chance kuma kike naima inji salma, kinsan already kinyi committing babban crime by impersonating a dead person , wlh d earlier d better, ki gayamai da wuri tun kafin yaji abakin wasu, “Jikin kursum yay sanyi ba kadan ba, dole ta gayamai yau idan yazo,” kawata nagode sosai da shawaranki, salma tayi murmushi, Allah yasa adace kawai, nizan wuce yanxu, kidai tabbata kin gayamai, kursum tace toh, ta mike ta raka salma har bakin gate, salma tace wai make faruwa ne, dazu naga wasu mata da niki nikin akwatuna sun shigo, “Haba dai nikam banga kowa ba inji kursum Salma tace OK sai dai munyi waya, sukayi sallama ta wuce. Samira!! samira!! ” da sauri ta fito daga kitchen, gani Antee sumy, kursum tace ina hanifa ? , tayi bacci nakaita daki…. “wasu mata ne sukazo dazu bansani ba? samira tace yan’uwan gimbiya, biki suka zo , suna bangaran baki kursum ta kwalalo ido waje, wa xaiyi aure a gidan nan ? ,”Antee baki da labarin baba shehu zai auri gimbiya gobe… ” kasa magana tayi dan takaici, afusace ta wuce dakin gimbiya Gimbiya na baje adaki sai lissafi kayan dazata siyo take, kursum ta bango kofa ta shigo, tafara wurgi da kayan gimbiya, yau dole kibar gidan nan, gimbiya tace kursum miye haka ? “Ta wurga mata harara, ban taba sanin ke makira CE ba sai yanxu, ashe ke kika tura acewa ex mijin sumy tayi aure tabar gari, toh yau karya ki takare dan nima yanxu xan fasa kwai, ke kibar gidan nikuma dama nasamu mijin aure. “Gimbiya tayi tsuru tsuru tabbas dagaske kursum take ba alama wasa, tana iya wurga ta waje, ta nisa tace kursum kiyi min hakuri nasan nayi laifi, ki bari idan na auri Shehu saiki tona asiri. Kursum data gama kulewa tace baki isa ba, u must leave yanxu nan, ta shiga tura akwatu nan ta waje, ” gimbiya dukta gigice tarasa abun cewa, can dabara ta fado mata, tace kursum naga mahaifiyar ki……. “Chak ta tsaya, karya kike, so kike ki raina min hankali gimbiya tace wlh dagaske nake, ta zazzage kayan ta, ta dauko wani karamin pink hankie da takarda aciki ta mika mata Kursum ta amsa, na miye wannan? ” tace mahaifiyar ki taban ranar data kawoki wajena, “da sauri ta bude, ba wasu rubutu masu yawa bane, ” kursum aka rubuta daga sama, daga kasa akasa lovely Mom…… Agigice ta kalleta, wace ce mahaifiya ta? “gimbiya tace ba kowa bace face umma dake zuwa gidan nan…… Dammm, lokaci guda zufa yafara keto mata, umma !! umma!! ta kira yafi a dirga, Umma y did u abandon me, u’r such a nice woman, ” kuka kawai take hankali tashe, sai yanxu ta tabbatar shakuwar su da umma ba abanza bane……… *Xarah Bukar* *Dedicated to Bady social* ~luv u all~ [16/09 10:09 pm] Xarah bukar : KURSUM by ~Xarah Bukar Page Ta dago idonta daya sauya launi tsabar kuka, ta kalleta tace kin cuceni, kinsan umma ce mahaifiyata shine kika boyemin har nayi falling in luv da yayana na jini bansani ba, Y ?, miyasa kike min haka ?? “Gimbiya tayi wiki wiki da ido, kiyi hakuri, mantawa nayi ban gayamaki ba, tunda yanxu kin kasani ba kuka zakiyi ba, tattarawa zakiyi ki koma gidan ta….. Haushi da takaicin kalamata ya hana kursum ce mata uffan, afusace ta fice takoma dakin ta …. Baba shehu ne tare da abba suna xantawa, “abba yayi dariya yace nazo nai mawa da’na aure ashe kaima auran xakayi…..” Yayi yake yace kasan aure lokaci ne, idan yazo dole ayi, ashe ya’yan namu sun shirya sai aure kenan, “Abba ya murmusa, shine dai ya nace yana sonta ,kasan yaran zamani sai abunda suke so ” baba shehu yace ai gwara ayi auran nan da sati biyu zaifi, dan nagaji daganin zainab ba aure, “abba ya numfasa, ba zainan nake nufi ba, yar wajan hadiza data dawo kwanaki nake nufi, ” dif annurin fuskan baba shehu ya dauke, aranshi yana mamakin karfi halin irin na alhaji Imam, wato karuwa ya zaba akan yar’sa….. Ya kirkiro murmushi dole yace xainab da sumayya duk ya’yana ne, karma ka wahalar dakan ka, na bawa danka ita har abada, idan kun shirya ana iya auran asati biyu kacal…. “ba karamin dadi Abba yaji ba, burinsa bai wuce yaga yazid yay aure, yama baba shehu godiya sosai Burinsa yaga yazid yay aure, suka tsaida rana nan da sati biyu kacal, sunyi hira sosai, daga bisani daddy yamai godiya ya fice. Baba shehu kaman ya fasa ihu dan haushi, da sauri yay dialling no din p.D…. “hello detective ya ake ciki ne ? p.D yace Alhaji munata bincike dai, nan da sati daya zan kawo report din komai… ” okay, ka gaggauta cox we are running out of tym, p.D yace ba matsala munsa kan aikimu. Har dare tana zaune a daki ba mafita, taci kuka harta gaji daga bisani ta tashi ta dauro alwala tahau salloli. Washe gari aka daure aure baba shehu da gimbiya, babu wanda ke farin cikin aure, “sai shewa suke a parlour suna dariya, Hinde kawarta tace wai ina masu gidan ne ?? naga tunda mukazo babu wanda ya tarbe mu ” gimbiya taja tsaki, aini ba ruwana dasu tunda nazama matar gidan, ina samun dukiyar su xan gudu bazasu kara gani na ba….hinde ta kwashe da dariya, gaskia kawata kinyi dabara , ko gidan nan kika samu kin more ba kadan ba, nidai kima mijin naki magana yay employing dina a company dinsu, “gimbiya ta balla mata harara tace keda kike nurse a psychiatric hospital miye na kwalaman aiki da mijina, indai aiki kikeso xan baki, Wana aiki zaki ban ? “ta murmusa tace aiki ne mai sauki , kinga nurse din hajiya ta tafi jiya, so xaki zama in charge of kula da lafiyan ta da bata magani Hinde ta bata rai, shi maganin bata iya sha sai an bata…..gimbiya tace ke wawiya ce wlh, maganin dazai gusar mata da kwakwalwa nakeso ki bata, kinga idan dosage yamata yawa zata fara hauka saimu kaita psychiatric, shine kadai zaiza insamu dukiyar gidan nan hankali kwance:) ” kin samu dukiyar ni kuma fah ? inji hinde, “haba kawas idan nasamu 50-50 xamuyi mana Hmmm kawai hinde tayi, tasan halin hafsatu da kudi, amma zatai aikin. Shiga na alfarma tayi ta fito rike da hanifa, ta leke dakin hajiya, chan ta hangota kwance kan gado tana bacci, karasa wa ciki tayi ahankali, ta kare mata kallo, aranta tace Allah kadai yasan maike damun hajiya, ta lura she is alwyz depress, ta janyo blanket ta rufeta sannan ta fita Tana sauko wa suka bita da ido, ko kallan su batai ba tayi waje, hinde tace itace kursum ? “gimbiya ta yatsine fuska, itace fah, amma banda case da ita already matsalolin rayuwa sun mata yawa. Yana zaune cikin mota, ta bude ta shiga, ta kalleshi tai murmushi, sorry 4 keeping u wait “ya lumshe sexy eyes dinshi yaja mota ,yace am not complaining, ya taba cheeks din hanifa, cutie bakya magana sai murmushi alwyz, ” kursum tace datz wat u have in common, kasan jini baya karya “yace I don’t understand, jinin wa kuma ? Da sauri ta share xancen tace I cnt wait 2 c umma, kwana biyu nayi missing dinta, plz ya yazid mu tsaya shoprite ensai mata sumtin special ” yay murmushi, toh yar umma, ni kuma mi zaki siyamin ? “caraf tace nothing, amma xan siyawa sister dinka chocolate… ” banda sister ai, ni kadai umma ta haifa a duniya, so dat chocolate belongs 2 me… “Jikinta yay sanyi, dama da gangan tamai batun sister dan taji mai xaice, she has to b sure ko dagaske umma ce mahaifiyar ta Sun iso shoprite, ya kalleta da alama tayi zurfi cikin tunani, ya tabo ta, ” hey are u alright ? “firgigit ta dawo hayyacinta, hmm yea am okay ” yace muje koh tace toh… Siyayya na gani na fada tama umma, ita kanta batasan iya adadin turaruka da super wax din data kwasa ba, taje counter akamata package din komai, ta mika credit card dinta, daya daga cikin agent yace madam ur bill is settled “Okay kawai tace tasan shine ya biya, yana tsaye awaje tare da hanifa…… Hankali kwance ta fito, bata Ankara ba taji an bangaje ta, tana dagowa sukai 4 eyes da zee tare da meerah, ” zee ta kalle meerah, galfrnd ga karuwar data min snatching ya yazid, meerah data shagala da kallon kursum tace not bad, she is pretty, so I don’t blame him.. “Rai abace kursum ta balla masu harara, tace zee banda lokaci, bad behaviour dinnan naki yasa ya yazid yayi dumping dinki a dustbin, ” zee tai kwafa tace cousin sis ur dayx are numbered, tsakani na dake zamuga waye bad person, kuma ki rubuta ki ajiye nice matar ya yazid bake ba.. “hmm kawai kursum tace, ta raba ta gefe tawuce… ” meerah tace galfrnd dole ki susuce, ur sis is damm pretty, I tot ko irin village gals dinnan nan tsaki zee tayi, kizo mu fara shopping kar dare yayi, ko kema kin kamu ne ? “Aaah haba dai, kinsan kece tawa Koda ta dawo bata nuna mai ta hadu da zee ba, sai murmushin dole data kirkiro, yaja mota har gidan umma….. Umma na zaune a parlour suka shigo, ba karamin dadi taji ba, dan batasan da zuwan su ba, “har kasa kursum ta duka suna gaisa, ta amshi hanifa dake bacci tace yaudai sumy tazo gidan ummata, ” kursum sai sunne kai take, gabadaya she is not comfortable saboda wani irin mayataccan kallo da ya yazid ke mata, “umma dake lura dasu ta kalli ya yazid tace my son na bar glasses dina a mota jeka dauko min, sum sum ya tashi, umma tai murmushi, daughter sannu da kokari duk kayan nan nawa ne ” kursum tai shuru, ita dai abunda ya kawota gidan bai wuce tasan ko umma ce uwarta ba, Umma tace ga hanifa kaita dakina ta kwanta, barin duba masu aiki a kitchen “tace toh, ta amshe ta.. Tana shiga dakin ta ajiye hanifa kan gado, ta zuge jarkar ta dauko dan karamin paper da gimbiya taba ta, ta kalli rubutun, aranta tace dole ta binciko any note mai rubutun umma dan tayi comparing ko ita ta rubuta…. Da sauri tahau bincike, taja side drawer taga magazines dayawa, ta fiddo su gabadaya tana dubawa, dakyar tasamu karamin memo mai rubutu aciki, tayi comparing, sam baizo daya ba, nan take tafara zubda hawaye ” bata Ankara ba saiji tayi umma tace lafiya kikemin bincike ? Agigice ta juyo ta kalleta, tace umma plz ki gayamin gaskia ke kika haifeni ? umma ta kwalalo ido, bangane mai kike nufi ba ? “Kursum ta mika mata karamin paper din, tace kin tuna wannan ? Umma ta karba ta duba, ta kalli kursum a tsorace tace ina kika samu paper dinnan ? wace CE ke??? *Xarah Bukar* *Dedicated to Bady social* ~Luv u all~ *KURSUM* By ~ Xarah Bukar Gaba daya ta kidime, dakyar ta maido da hankalinta tace umma kawata da mukai accident nake nufi, gimbiya tacemin ke kika kaita wajenta 18yrs back “umma ta bata rai, kin sani aduhu, bangane xancen kiba ” ta karaso gabanta ta tsuguna, umma nasan kinsan komai, ki taimakeni en cikawa kursum burinta na sani wace mahaifiyarta, plz help me….. “ta sauke dogon ajiyan zuciya,ta dagota suka zaune kan gado, tace sumy ki daina kuka, nasan baki da aminiya data wuce kursum, amma kisani bani na haife taba, asalima taimaka mata nayi na kaita wajan gimbiya….. ” kursum ta dafe kirji, umma wace ta haifeta? Ina take ??? ” tabbas tana garin nan kuma da ranta, saidai nai mata alkawarin bazan taba gayawa kowa ba, sai kiyi hakuri da cikar burin kawarki, iyakacin abunda xan iya gayamiki kenan…. Hankalinta yayi matukar tashi, jikinta har wani kyarma yake, fatan ta bai wuce Allah yasa data da mom dinta ba, atleast taji dadi ya yazid ba yayanta bane, “cikin tsananin damuwa ta dago ta kalli umma, tace nagode sosai koba komai yanxu nasan bake kika haifeta ba, ” tai murmushi tace daughter banson ganin ki cikin damuwa akan abunda bai shafeki, kinga aure zakiyi, ki ajiye past aside kiyi focusing on ur future “toh kawai kursum tace… Turus yayi ganin fuskokin su da damuwa, da sauri ya ejiye glass din akan drawer, ya karaso yace umma hop all is well, ” ta balla mai harara, babu ruwanka tsakanin mune, koh sumy ?? Kursum dai murmushin dole ta kirkiro, batace komai ba, ya yazid ya kalleta, cry cry baby, bana hanaki kuka ba “ta shagwabe fuska, ni banyi kuka ba, kawai dai am feeling dizzy…., ” caraf umma tace muje kici abinci kisha magana, ta mike taja hannu kursum sukayi parlour, ya yazid dake tsaye yabisu da ido, yarasa wani irin so umma kema sumy, ko yaushe bata da xance sai nata. Ta saki jiki sunyi hira da umma sosai, bayan magrib ta mata sallama zata wuce , ta dauko mayuka da sabulai masu tsada ta bata, ba karamin dadi kursum taji ba, tai mata godiya sosai. Suna shirin fita Abba ya shigo, ta gaida shi da fara’arta, “ko kallan ta baiyi ba, ya amsa a takaice ya shige daki , jikin ta yayi sanyi, tarasa dalilin dayasa abba bai sonta, daga ya yazid har umma basuji dadi ba ,haka dai suka fice a sukwane Alhaji narasa miyasa baka son yarinyar nan, ko gaishe ka tayi dakyar kake amsawa, abba ya nisa yace bata da mutunci ne, kirikiri ta sauke shehu daga MD ta maida kanta, alhalin ita ba komai tasani a harkar company dinba, Allah yaga zuciya auranta da yazid bai dadarani ba, kece dai kika nace ayi, “shiru kawai umma tayi, ta lura kota mai bayani bazai gane ba Ba wanda yace uffan, kowa da abunda yake sakawa a zuciyan shi har suka iso gidan, Ya amshi hanifa suka shiga ciki, parlour tsit ba kowa, ya janyo ta jikinshi yace nasan u are hurt da yadda abba yay treating dinki, “hmm am not, na dauki abba tamkar ubana, komi yamin bazan taba damuwa ba.. ” yay murmushi, I love u alot and I do appreciate ur respect towards my parents,”tayi shuru tana tunanin kodai ta gayamai ne, ta nisa tace ya yazid akwai important abu danake son gayama.. “Ina jinki, wat is it ?? ” ta sauke doguwar ajiyar zuciya sannan tace ni ba wace kake tunani bace, asalima ni ba yar gidan nan bace kuma hanifa ba ya’……shss ya katse ta da hanzari, nasha gayamaki ki ajiye past dinki aside let focus on d future, alot of people make mistakes in dia lyf no one is perfect, basai kin gayamin komai game dakeba, no matter abunda kikai bazan guje kiba…. “Ba karamin dadi kursum taji ba, koba laifin tasan bazai guje taba, tayi murmushi tace I love u more, ” yay dariya yace 1st tym in history my witch tace tana sona, itama dariyan tayi ,yamata gud nyt ya koma gida.. Ta kwantar da hanifa a daki sannan ta shiga dakin gimbiya, zaune take gaban dressing mirror tana tsansara kwaliya, “kursum ta shigo ta kare mata kallo, ke kuma ina zaki adaran nan?? ” gimbiya ta washe baki, dakin mijina xanje mana, ko kin manta nazama matar gidan… “Hmm Allah kadai yasan ya akai baba shehu ya yadda ya aureki, ni nasan sumtim is fishy, ” gimbiya ta balla Mata harara, koma dai minene anruga an daura, ya kukai da umma ?? “Kursum tace ba wani hop wlh, ba itace ta haifeni ba, tasan wace uwata, amma tai mata alkawarin bazata fadi ba, dan haka nidai xan cigaba da bincikawa tunda tacemin tana garin nan… ” gimbiya ta yatsine fuska, wai bazaki hakura da naiman taba, uwar nan taki bata da mutunci, inda tana sonki data nemoki da dadewa, “kursum ta bata rai, ya isheki haka, karki zagan min uwa, dukda ta jefar dani I don’t hate her, am sure tana da reason.. ” toh saiki nemota ai tunda baki da zuciya, ni kinga tafiyata , ta feshe jikinta da turare ta wuce dakin baba shehu….. “kursum dake tsaye ta bita da idanu *Xarah Bukar* *Dedicated to badia* ~Luv u oll~ [04/10 6:12 AM] : [19/09 8:35 pm] Xarah bukar : *KURSUM* By ~ Xarah Bukarêê Bayan sati daya Tunda kika zo kike bani magani duk bayan 2hrs, na miye wai?? “nurse hinde tace hajiya kwantar da hankalinki, duk magani lafia ne, doctor yace abaki…. ” nikam kwanan biu nan banajin dadi jikina , surutai nakeji cikin kaina, da alama drugs dinnan ke naiman haukatani, “hinde dake faman hada liquid Budeprion da Desyrel ludiomil a syringe, ta mike ta karaso gaban ta zata tsira mata allura, ” ba shiri hajiya ta mike tsaye, wannan fah, shi kuma na miye ??? Galala hinde ta kwalalo ido tana kallonta, ashe ba makauniya bace kina gani, “hajiya tace kinason kashe ni ai dole in taimaki kaina……ahh lailai kam, ai tunda kika gani toh saina tsira miki shi, da karfi ta damki hajiya ta tsira mata alluran a wuya, luuu hajiya ta fada kan gado, stars kawai take gani har bacci ya kwashe ta…… Hafsatu!! Hafsatu!!!!, da sauri gimbiya ta fito daga daki, hinde lapia kike kwallamin kira,”hinde ta balla mata harara, kinsan dai babu secret tsakanina dake, shine kika cemin hajiya bata gani ashe karya kike….,”sorry mantawa nayi ban gayamiki ba, yanxu tasan kinsan tana gani ne?? “tasani mana, amma idan ta tashi she will b confuse ,alluran danai mata is very strong, gambiya tayi dariya, haka akeso ai, gidan mahaukata ne daidai da ita…..Hinde kam tsoro yakamata kar hajiya tasamu sauki asirinta ya tonu, zata dakata da yi mata alluran, ta kalli gimbiya tace ina kursum yau bangan taba?? ” taje office kinsan kwana biyu bata jeba Hmm ita da auranta nan da kwana hudu miye na zuwa office, kodayake banga ana shirin komai a gidan ba “gimbiya tace aifa babu wani shiri, gidan nan fa babu mai sonta, uwar mijin ce keji da ita kaman ranta… Nifa nagaji da jira, baki gama aikin bane? “yi hakuri salma yanxu nan xan gama, wasu files din kusan 3weeks kenan ban duba ba…,” hanzarta dai kinsan 6 ake rufe kasuwa already 4pm har yayi…. “toh kawai kursum tace ta mike da sauri, kinsan nima nabar hanifa wajen samira, dole muje sharp sharp mu dawo… Sun fito kenan suka hadu da zee zata shiga, ko kallon su batai ba ta kutsa ciki… Salma tace zee na aiki anan ne ?? ” a’a ba tayi gurin baba shehu tazo, ta dade da barin gida ai, gidan kawarta meerah take zama.. Allah ya shirya salma tace, kodayake babanta ya barta take abunda takeso, yauwa kursum ya kukai da ya yazid kin gayamai?? “kursum ta nisa, wlh nayi kokarin gayamai shine baya son xancen, bayan auran dai zan gayamai…,salma tace toh da anyi auren ki tabbata kin gayamai tun wuri, ” okay kawas xanyi hakan. Rai abace ta shigo office dinsa, ko gaisuwa babu taja chair ta zauna, baba lafiya kace inxo yanxu ?? “baba shehu yay murmushi, zainab yau fushi ake dani kenan, ” ta kara tamke fuska, baba dole inyi fushi, miyasa ka auri gimbiya? Ya kwashe da dariya haba yar baba, karki damu akwai dalilin dayasa na aureta, nan gaba zata yi amfani, “Tam naji ya ake ciki, hop dai detective ya kawo report ?? ya miki mata pictures din dake hannusa…ta amsa ta duba, picx din sumy da wata ne, tace baba bangane dayar ba wace ? Baba shehu ya nisa yace sumayya ce ta asali wace ta rasu, wace take gida itace ta karya, sunanta kursum ” ta kwalalo ido waje bangane ba… yace dama nasan bazaki gane, ya dauko wasu papers acikin file ya mika mata, iya kacin taimakon dazan iya miki, ki karanta, bayanin komai naciki…,ta karba da sauri, ta mike tsaye tace baba nagode sosai , da gudu ta fice daga office din Baba shehu yay murmushi, lailai yarinyan is smart, yar karama da ita tayi fooling kowa, shi kuma yazid ashe ya tabayin aure, hmm sudai suka jiyo, nikam nazama legal owner of diz company.. Garin sauri motar ma awaje tayi parking, ta shigo gidan da gudu tana kwallawa meerah kira, meerah dake wanka ba shiri ta watsa ruwa, ta fito da sauri daure da towel, “zee wats wrong, miye kike ihu….zee tace galfrnd sa kaya mu tafi kawai….” Ina zamu je??….”gidan su ya yazid, yau asiri ya tonu, ashe sumy impostor ce, ta mika mata picx din…meerah ta kalla taja tsaki wlh galfrnd baki da wayo, idan kin gayama su aiba abunda zasu ce, dan ba karamin sonta suke ba “Jikin zee yayi sanyi, tabbas haka ne, ta fito da papers din tace galfrnd zauna mu karanta, ko zamu samu wani abu…… Suka hau karance karance, “meerah ta nisa, tab diz is serious so sumy da kursum are best of frndz, suddenly ya yazid appeared n married sumy, daga karshe ya gudu ya barta da ciki, ” zee data gama kulewa tace I cnt believe ya yazid betrayed me, muna dating yaje kauye yayi aure bansani ba…”meerah ta kwashe da dariya, ga wani interesting part of d story, bayan 9month original sumy ta haife baby gal, aftet one year zasu zo kano sukayi accident, sumy ta rasu, kursum tayi surviving……”meerah ta kara kwashewa da dariya tace ita kursum bata da kowa aduniya datx y tayi deciding using dead person identity, babban crime kenan “Zee tace sai yanxu nagane komai, hanifa diyar ya yazid ce, ita kuma kursum tazo seeking revenge akan dumbing kawarta da yayi, datz y takeso ta auri shi, ” meerah tace exactly, duka love din da take nuna mai is 4 pay back, idan ta aure shi saita rama… Zee tayi murmushi, no wonder first tym data ganmu tare tana ta zaginshi kaman dama tasan shi, ashe dai sun taba crossing path, Ohh she is really smart, ga auran su nan da 4days zamuga wa zaiyi saving dinta, “meerah tace game over, yanxu shiru zamuyi, sai ana gobe daurin aure zamu tona asiri…. ” haba dai y not ayita ta kare yau…..”ke dai kisa ido kawai, kinga idan yasan gaskia he will b hurt ke kuma lokacin zaki samu daman mallake shi, ita kuma kursum crimes dinta sun isheta bakin ciki…… “Suka kwashe da dariya, zee tace criminal babba kuwa, identity theft,fraud, da kidnapping duk ita kadai Oh ni xarah harda su kidnapping:oops::oops::oops: *Xarah Bukar* *Dedicated to badia* ~luv u oll~ [04/10 6:12 AM] : *KURSUM* By ~ Xarah Bukar Bayan kwana biu I dont know y kike dulling lyf dinki, ga arziki kin tara ta ko ina, amma kinki sakin kudi ayi bushasha, gidan so boring kaman ba buki akeba, acewar gimbiya, “kursum tace kashe kudi is not nessacary, albarka aure nake naima, shiyasa na gaya mai ba event din daza muyi, simple wedding ya isheni,” hmm haushi da takaici ya hanata maida mata martani, tabbas idan ta tsaya kallon ruwa kwado zai mata kafa, yarinya karama sai wayo, duk dabara ta nakasa tsatsan taro gareta, amma xanyi maganin ta, tsum tsum ta tashi ta fice….ita dai kursum ko ajikinta, ta cigaba da hada kayanta waje daya, chan wayanta yayi ringing ta duba, inna sadiya ke kira,da sauri ta dauka, inna har kin iso? “eh gani awaje, kizo ki shigo dani…..toh gani nan fitowa, ta kwallawa samira kira, “da sauri tazo, gani antee , ” tace zauna da hanifa, barin je waje indawo, ta fice da fara’arta yaudai xataga inna, tana saukowa parlour zee da meerah na shigowa, ko kallansu batai ba tayi waje, “meerah ta kwashe da dariya, oh boi dis ur sister gather confidence no b small, zee tace sister 4 wia, abeg daina hadani da ita, gobe by diz tym revenge will b served…. Tana ganinta ta kara fadada fara’arta, sukai gaisuwan yaushe gamo, ta riko ta suka shigo gidan, tace Inna ya naganki ba kaya kodai ba kwana zaki yi ba ?? Inna tayi dariya, ana bukin ya’ta ai dole in kwana, dayake yayata nada gida anan shiyasa nace barin sauka can, tunda ba kowa gidan, lagos take zama yanxu, ” kursum tace amma dai nan zaki na wuni ai har agama buki koh?? Inna tace eh mana, saidai gidan shuru, banga alama ana wani shirye shirye ba, “ai babu wani shiri, yan gidan babu ruwansu da kowa… ” toh fa, Allah shi kyauta inji inna.. Suka shigowa parlour taga samira na mopping, a firgice tace mi kikeyi anan ? Ina hanifa ?? keda nace ki zauna da ita har indawo…..”samira tayi wiki wiki da ido, tana wajen antee zee….wat kursum tafada akidime, da gudu tahaura sama, “zee rike da hanifa sai jajja mata cheeks da dungure mata kai take, shegian yarinyan ko kuka batayi sai murmushi like Christmas goat, meerah tace ubanta ta dauko, bakiga kamar su ba,”tsaki zee tayi, wlh I feel like killing her, ” wat ya’ta zaki kashe ina raye, toh wlh baki isa ba, “atsorace suka dago suna kallonta, sam basu San da shigowarta ba, ” da sauri ta karasa ta amshe hanifa, ta nuna zee da yatsa don’t u ever threaten my daughter, infact ko da wasa karkiyi gingin daukar ta, “zee tace kai sis wasa kawai muke da ita, ” ta balla musu harara, Ku ficemin daga daki banason crazy people around me, caraf meerah tace ennn don’t try me, c diz small gal oooo, oloshi olori buruku, karki kuskura ki zageni, kuyi sister drama tsakanin ku karki sakoni ciki, “tam naji, ku fice min plz….afusace meerah taja hannun zee suka fice… Kursum ta sauke dogon ajiyar, Allah yasa na iso dawuri da bansan mi zasu mata ba, ta fito zata koma kasa sukai kicibis da gimbiya a stairs, fuska a murtuke tace naga mai kitson ku a palo, ina fatan ba arziki tazo ci ba, “ta nisa, tace inna tafi karfin kice mata mai kitso, kin dauka kowa irinki ce, toh kisani buki tazo ba gulma dasa ido ba….tasss kawai kake ji, gimbiya ta wanke ta da hot slap, ni kike gayawa maganan banza……caraf umma tace ai ba karya taiba, ki mareni idan kin isa,” gabadaya sun firgita, “da kyar kursum tace umma yaushe kika zo ?? ” nayi kusan 5mins da zuwa, zan hawo naga ta wanke ki da mareni, toh wlh bazan zauna ana mistreating daughter in- law dita ba, ta kara kallon kursum akaro na biyu tace maza hado kayanki mu tafi, gidana zaki zauna har agama buki, idan an daura kya koma gidan mijinki, ” umma kiyi hakuri…. Kimin shiru kawai, idan har na isa dake zakibi umarni na, zan shiga wajen hajiya, 15mins na baki ki hada komai naki kafin in sauko…fuuuu ta wuce abunta, “gimbiya tayi dariyan mugunta, ai gwara ki bita, zamanki gidan nan bashi da amfani, ” kursum dai shiru tayi batace uffan ba, ta sauko parlour taba inna rikon hanifa takoma daki dan hada kaya….. *Xarah Bukar* kursum 64 to 65 Posted by XARAH ABUBAKAR on NOVEMBER 13, 2016 *KURSUM* By ~ Xarah Bukar zaune take adaki tana zuba surutai marasa gan gado, hinde dake gefe tace barin kawo miki abinci, ta mike ta fice, umma ta turo kofa ta shigo, da sauri ta dago, tai murmushi tace mairo kina nan ashe, kusan sati biyu kenan ina jajanki, “ta bita da ido, yaushe kika fara gani bansani ba…”hajiya ta gyara zama tace ai ban magance ba, idanuwa na garau suke, dama karya nayi , “lailai ma hadiza kin raina mana wayo, shekara da shekaru kina gani ashe, ” ta kara gyara zama tace nagaji da boyewa shiyasa naga ya miki, mijina da ya’ta sun mutu so banga dalilin dazai sa incigaba da pretending ba, “umma ta nisa, tace gimbiya munafuka ce ashe ta gayawa sumy nice nakai kursum wajanta, shine kwanaki ta ke tambaya na ko nice na haifi Kursum…..” Kaga yarinya da bincike, me kika ce mata ??? “ban gayamata ke kika haife taba, koda tayi insisting cemata nayi tabar xancen tunda kursum din ta riga ta rasu, ” gimbiya da hinde dake labe bakin kofa sukai turus jin abunda umma ke cewa, da sauri hinde taja ta suka bar wajan,”tace dama hajiya ta taba haihuwa ?? gimbiya tace nima dai nayi mamaki, ban taba jin labari ba, amma kuma yanxu komai yay making sense, yar’ da umma ta kawo min itace kursum, su atunanin su kursum ta mutu not knowing itace ce anan, “hinde tace maza muje mu gaya mata hajiya ce uwarta, gimbiya ta watsa mata harara, so kike ta wurga mu waje mu tashi a tutar babu, ba kudi ba gidan zaman, ai kawai shuru zamuyi, ” gaskia kin kawo shawara mai kyau inji hinde…. Nikam na yanke shawara gidana zata koma, tunda ba kula da ita kuke anan ba, hajiya taja tsaki, ai tuntuni na hanata shigomin daki, kusan sati kenan banganta ba, “na rasa miyasa bakison ta,kiri kiri kike nuna mata tsana….” Ban tsane taba, kawai dai her face looks familiar, nasha ganinta a mafarki tana kuka, I donno knw y…..umma tace Allah shi kyauta, ni zan wuce kinsan mune da biki, nabar baki agida, sukayi sallama ta fice…. Zaune suke a palo suna hira, umma ta sauko, muje koh…..suka mike, kursum ta kira samira takai mata kaya mota…….”mata nan akwai kinibibi, “zee dake zaune tana danna waya tace wace mata ? taso kigani, ….da sauri ta tashi, suna leki ta window, ta buga uban tsaki, anya umma bazata ruguza mana plans ba, a day 2 d wedding miye na kaita gidan ta, ” meerah tace calm down, gidan muma zamu gobe ayita ta kare, zamu ga karshen soyyaya ai…..Umma da kursum a gaba tana jansu, inna rike da hanifa abaya.. “gidan shake yake da yan’uwa da abokan arziki, umma sai fara’a take tana nunawa yan’uwa surukarta, suna mata tsiya ta masu wayo tasamu kakkaywan yarinya, “gabadaya kunya ta rufe kursum, da kyar ta iya gaida su…..” umma tajata sukai part dinta, dan nanne ba jama’a, “tace dakina zaki zauna har agama buki, duk abunda zaki bukata zansa akawo miki, aladabce kursum tace toh umma nagode sosai,” inna dake gefe tace yamma tayi xan wuce, tunda nagane gidan gobe xanzo da safe,”umma tace ba matsala, barin kira driver ya kaiki….sukayi sallama ta fice…. Karfe 11.15pm tana kwance takasa bacci, ta dau dairy dinta tafita kitchen hada tea….”zaune yake kan dining yana shan coffee, ta shigo palo ta zaune sam bata lura dashi ba, ya bita da kallo sanya take da armless nyt wear iya gwiwa, gashin kanta daure da pitch ribbon…yaushe tazo gidan nan ?? ya tambayi kansa, da safe sunyi waya batace zata zo ba, tun dazu kuma her line is off, “ya kalleta akaro na biyu, rubutu take a dairy din, chan ta nisa ta ajiye gefe, tahau tunani…aranshi yace ko tunanin mi take ?? (nidai nace oho), ya mike ahankali yaje ta bayanta ya zare ribbon din kanta, afirgice ta dawo hayyacinta, zata kwalla ihu ya janyo ta jikin shi yasa hannu ya toshe mata baki, dukta kideme dakyar ta iya cewa ya yazid u startled me, ya matse ta tsam yana lumshe ido, gaba daya she is not comfortable da rikon da yay mata, har numfashin su na naiman hadewa….ya matso da lips dinshi zai sumbaceta tayi saurin rintse ido, jikinta ya hau rawa, itakam she has never experience sumtn lyk diz….ganin reaction dinta ba shiri yadawo hayyacinsa, da sauri ya saketa, ta ruga daki da gudu tana maida numfashi, “lokaci guda ya shiga wani irin yanayi dabai san namiye ba, ya sauke doguwar ajiyar zuciya, ya dau pen da diary din ya fice part dinsa…. Washe Gari Gidan so bizy, sai dafe dafe da gyare gyare ake, salma da inna tun safe suka zo anata hidima, “kursum na zaune a palo taci uban kwalliya cikin hadaddan turquoise blue lace mai ratsin pink, yar borno dake mata lalle tayi dariya tace gaskia amarya yadda fatar nan taki ke sheki ko a kasar larabawa sai hakaaaa…..da gudu inna ta shigo tace yau mun shiga uku, ” kursum tace lafiya dai koh ?, inna tace ba lafiya, yan sanda kusan su takwas nagani a haraban gidan, ba shiri kursum ta mike muje mugani Allah sa lafiya dai…..suna fita sukaga umma da abba atsaye suna bayani, abba yace saidai ko wrong house kukazo, mudai bamu da mai suna kursum agidan nan…..dammm gaban kursum ya buga, daidai lokacin yazid da huzaifa suka shigo gidan, zee da meerah dake gefe suka karaso, zee tace ga criminal din arrest her…,ya yazid ya balla mata harara, u are crazy akwai wanda yayi kama da criminal anan ?? tace kwarai kuwa, ta nuno ta da yatsa tace wannan yarinya itace kursum, ba shiri dan sanda ya fiddo da handcuff, “you have the right to remain silent, anything u say can and will be used against you in a court of law……. *Xarah Bukar* *Dedicated to Badia* *KURSUM* By ~ Xarah Bukar 65 Duk suka bi kursum da kallo, suna jiran bayani daga bakinta, itako shiru tayi banda zubda hawaye da take….. ya yazid ya karasa gaban ta, ya kalli dan sanda a murtuke, officer sai dai misunderstanding aka samu, her name is sumy not kursum, officer ya zaro paper daga aljihu yace ga arrest warrant for identity theft, fraud & kidnapping, “gaba daya ya shiga duhu,dakyar ya iya cewa diz cnt be possible, ya kalle ta, watz going on ?? ,da sauri zee ta tari numfashin shi, ta tsara mai komai tun daga farko har karshe, ” ba karamin gigicewa yay ba, dukda yasan ba karya acikin abunda zee tace ya kasa gasgata zance, “zee ta mika mai pictures din tace daukar fansa tazoyi, kai kamu ka fada trap dinta so easily, worst part of it shine yar’ka hanifa tada boye ma…..” Ya karewa pic din kallo, dukda shekaru sunja bai hanashi tunawa da fuskar taba, ya kalli na kursum tabbas her face has alwyz bn familiar, sai yanxu yaganeta, itace ta mareshi first tym da suka hadu, amma shi bai taba sani dey are frnds wit sumy ba,Ya dago idonsa daya sauya launi ya kalleta, I cnt biliv u played me 4 a fool, arauna ne tace yaya plz 4give me, I have alwayz loved u since d first tym we met, kayi hakuri ka bani chance……. hannu ya daga akufule, enough kimin shuru, kin riga kinyi breaking heart dina, so I have notin to do wit u, “officer plz kuwuce da ita, banason ganin face dinta……. Plz fans kuyi maneji da wannan wiyana ke ciwo *Xarah Bukar* *Dedicated to Badia* ~luv u oll~ kursum 66 to 70 Posted by XARAH ABUBAKAR on NOVEMBER 13, 2016 *Kursum* By ~ Xarah Bukar hankali tashe umma tace son karka ce haka, gobe daurin aure atleast ka bata chance, ” rai abace yace I’d rather die than 2 marry her, auran ne nafasa “ido jajir kursum tace yaya nasan u are angry, ko mi kamin I deserve it but plz karka rabani da hanifa, ita kadai na mallaka a rayuwata, ya wurga mata harara, baki da wata rayuwa data wuce ta prison, so keda hanifa har abada, “salma da inna dake gefe duk jikin su yay sanyi, abu da suke tsoro yafaru…..huzaifa yace calm down bro, kabari ayi komai cikin hankali, kar kayi abunda zaka zo kana regretting….Abba ya daka masu tsawa, banason xancen banza, officer kuyi abunda ya kowa ku, kubarmin gida, ba shiri suka sa kursum a mota suka wuce station, kanwar abba antee saude ta kwashe da dariya, Allah ya kara, ga namu ya’yan aka tsallake su, aka fita waje naima na titi, tunda anfasa auran bari mu tattara mu koma inda muka fito….Abba yace babu inda zaku, ya kalli umma, duk laifin kine, koda yaje yayi auran sa na farko banda labari sai daga baya kika gaya min, dan kunga Ina shiru shiyasa kuke min abunda kukeso, toh baku isa ba aure dole a daura game rabo, dan baza a mai dani karamin mutum ba,” lokaci guda umma da ya yazid sukace dawa zaa daura ???, yace idan an daura gobe kwaji, na gama magana….fuuu ya wuce ciki afusace….shima ya yazid ya wuce daki rai abace, sai yanxu yasan zafin da ake ji idan aka yaudari mutum, “huzaifa ya kira salma su wuce, dan zamansu ba amfani…..” Meerah tace galfrnd let go, kinsan yau akwai celebration, zee ta murmusa, ki bari zuwa gobe, am very sure dani xaa dauran auran, suka kwashe da dariya suka bar gidan. Gidan tsit, kaman ana zaman makoki, gaba daya hankalin umma ya tashi, ya zama dole ta gayawa hajiya kursum na raye, dan ita kadai ce zata iya taimakon ta, da sauri ta dauki mukullan mota ta fice. *Police station* Hey pretty gal ki mana shuru, kinyi laifi an cafko ki kin ishemu da kuka, “ta balla mata harara, ina ruwanki dani….police woman ta gyara tsayuwa, tace kin shigo hannu, so karki kuskura kice zaki min fitsara, ta wurga mata kayan dake leda,na baki 10mins ki cire na jikinki kisa su… Umma ce zaune a office din d.p.o suna xantawa, tace ka taimaka ko nawane zan bada ayi realising dinta on bail, banason tayi kwanan cell, d.p.o yayi gyaran murya, gaskia hajiya her case is critical, yanxu an mata transfer to federal prison, dole sai an shiga kotu, shawarata shine Ku sama mata lawyer, idan kuma babu akwai lauyoyin gwamnati, suna iya tsaya mata, umma ta nisa, toh shi kenan zamu samo lawyer, amma da wuri mukeso ashiga kotu, “d.p.o yace indai akwai lawyer ba matsala, yau Friday zuwa next week ana iya shiga kotu, tace toh, xan iya ganinta ?? yace kwarai kuwa, ya kira sergeant, maza kaita cell 0644, sergeant yace ba kowa, duk suna mota xaa wuce dasu prison, d.p.o yace ok rakata waje, kafin su wuce, da sauri ta mike suka fice Prisoners ne wajan talatin sanye da blue riga da wando cotton, sunyi layi suna shiga katoton luxurious bus mai tambarin federal prison ajiki, ga yansanda ta ko ina a tsatsaye, sergeant ya kwallawa madam kofo kira (police woman dinnan), ta karaso tana cika tana batsewa, “oga yace akawo hajiya taga prisoner din da aka kawo dazu, ” madam ta karewa umma kallo tace tana cikin mota already, saiko ta window zaki mata magana na minti biyu kacal, umma tace hakan ma nagode muje, suna tafe umma tace madam officer nasan kune in charge of tsare prison din, taimako nakeso gareni, “wani iri kenan?? inaso ki kulanmin da yarinyan nan, banaso ta wahala a prison, ko nawa kikeso xan baki, ” madam ta washe baki, karamin aiki kenan, indai zaki bani dubu dari biyar cash, toh babu wanda zai taba ta, “umma tace nakara miki #200k asama, ta fiddo card dinta, gashi ki kirani, ki turo min account details dinki, zakiji alert as soon as possible, ” madam tace angama hajiya, suka iso bakin motan tace ga yar’ki can last window, minti biyu na cika xanja mota…..”tana zaune tayi tagumi, banda sharar kwalla da take, kursum!!! taji muryan umma na kiranta, da sauri ta juya taganta tsaye side window, tayi nairai da ido, umma kiyi hakuri ki yafeni, Allah yaga zuciya ban cuce kowa…..”shtss karki kara ban hakuri inji umma, nasan baki da laifi, duk abunda ya samu bawa Haka Allah ya kaddaro, shiyasa nakeso ki kwantar da hankalin ki, ina nan tare dake, “ta fashe da kuka, umma ina hanifa?? tana gida wajen inna, karki damu nace ta kula da ita….zata kara magana mota ta tashi, da Sauri tace umma ki cewa mamata ina gaishe ta….toh kawai umma tace a sanyaye, suka ja mota suka wuce…. Tsinan niya dama nasan da wani hidden agenda kika zo gidan nan,”ta kalle shi a wahalar ce, dakyar ta iya cewa shehu sake min wuya karka kashe ni, ya kara sheke wuyan dakyau yace kinsan cewa kursum ba sumy bace shine kika boye mana koh ? “gimbiya tayi tsuru da ido, bangane ba… yace munafuka ai bazaki gane ba, indai kinason zaman gidan nan dole kije kotu kiyi testifying karya akan ta, nafiso ta dauwama a prison, idan kunne yaji jiki ya tsira, yayi wurgi da ita kan gado, ya fice afusace, ” da sauri ta mike tsaye tana maida numfashi, ta karasa gaba mirror tana kallon yadda wuyanta yayi jajir tsabar damka, aranta tace ohh su kursum asiri ya tonu kenan, lailai ko dole tayi magani baba shehu, dan ta lura shima kwadayin arzikin yake, ta fito tana zake zaken azuci, xata sauka kasa taga umma ta shigo gidan, da sauri ta koma, ganin umma ta shiga dakin hajiya itama taje ta labe bakin kofan…..”hajiya dake kwace ta yunkuro dakyar ta zauna akideme tace kina nufin kursum ya’ta ce ?? kwarai kuwa itace bata mutu ba, ke kadai ce zaki iya kubutar da ita daga prison, hajiya ta sauke doguwar ajiyar zuciya tace nayi losing dinta d first tym, diz tym bazan bari ta kufce min ba, I have to save her, da sauri tadau waya ta kira barrister shu’aibu, “cikin minti 10 ya iso gidan, gimbiya dake labe tabar gun da sauri ta koma daki a kideme, idan kursum tabar prison kashin su ya bushe, dole tadau mataki… Barrister shu’aibu yace hajiya kwantar da hankalinki, wannan case din mai sauki ne, u’r her mom ke dayace zaki iya kubutar da ita daga zargin fraud da ake mata tunda she is d legal owner of d company, indai kikai testifying a court angama,” umma tace kasan harda identity theft, ya kenan ? yace inde xaa samu wanda xai bada good testimony akan relationship dinta da marigayiya toh she is save…..hajiya ta nisa tace ba matsala, gimbiya xatai testifying tunda tasan dey are best friends, yace toh shikenan, xanyi kokari zuwa Monday ashiga court, yamasu sallama ya fice, umma ma tamike yamma tayi zata wuce…. *Federal Prison* Babban prison mai dauke da 6 story building, kowa sanye da blue uniform, wasu na field suna playing basketball, daga gefe kuma wasu ganda ganda mata ke busa sigari suna caca…….new inmate da aka kawo sunbi layi ana nuna masu cell dinsu, “ana zuwa kanta madam kofo tace pretty gal ur cell is over dia, come wit me… atsorace kursum tabita abaya, danta lura da irin kallon da prisoners din ke mata…tayi pressing lock, cell din ya bude, tace ga naki, if u need anytn kimin magana, “kursum ta karewa cell din kallo, duk yafi sauran kyau da girma, gashi so comfortable, fully-furnished tare da A.c, television da fridge, ta juyo ta kalli madam, nagode sosai, tace don’t thank me, ki godewa mamanki itace ta biyani in kula dake, ” kursum tayi shuru tabbas tasan umma ce, Allah ya saka mata….”madam ta kira wata tsohuwar prisoner mai suna Lady D, daga nin ta kaga rikakkun mata masu duniya, gabadaya jikinta zanan tattoo ne , fuskan nan babu annuri, ga wasu prisoners uku na taka mata baya, “madam tace lady nabaki in charge of safety din yarinyan nan, ko kwarzano ban yadda amata ba, lady ta kalli kursum up & down tace expensive property koh ?? Kofo tace datx none of ur bizness, ki kulun min da ita kawai, “tace okay no p…. Kwance yake kan bed yayi ruf da ciki, gaba daya duniyar tamai zafi, kuka kawai yake hankali tashe, ya azabura ya mike yahau wurgi da pillows tare da naushin walls din dakin, afili yace ” y my witch, y did u betray me, kece rayuwata, d only gal I can die for…..yakara fashewa da kuka mai tsuma zuciya….umma dake tsaye bakin door ta karaso ciki da sauri ta rike hannun shi dake zubda jini, “agigice tace my son plz don’t hurt urself, kayi hakuri ka yadda da kaddara, komi yafaru is already written, ya dago idonsa daya canxa launi zuwa ja yace umma am shattered, d only gal I loved broke my heart, ” kar kace haka son, nasan she loves u alot, kodan darajan hanifa yakamata ka yafe mata, gashi kuma abbanka yace zai aura maka wata, ya zamuyi kenan ??? yace I don’t care, kowa abba ya daura min I will accept cox my daughter need a mother, “ta kalle shi da mamaki, tace u don’t care fah kace ? yace yes…..tace okay, ta fice afusace……ta iske abba a daki yana danna lapton, ta zauna a sanyaye tace Alhaji, ” ko dagowa bai ba yace ina jinki….,dan Allah dawa zaka daura mai aure gobe ? “Fuska amurtuke yace da zainab diyar shehu xaa daura, dama itace zabina tun farko….ta dafe kirji, alhaji kar kayi haka, yarinyan nan sam bata da kunya, ka taimaka ayi auran da kursum, itace zabin shi….” ya kara bata rai, tunda kinyi insisting, na yadda toh, zan aura masa zabina da zabinki, agigice tace su biyu zai aure ?? “yace eh amma on one condition, karki kara shiga lamarin Kursum na yanke alakar dake tsakanin ku, infact ko court kika je ko prison ganinta abakin auranki………..:oops::oops: *Xarah Abubakar* *Dedicated to Badia* ~luv u ol~ [04/10 6:12 AM] : [28/09 12:49 pm] Xarah bukar : *KURSUM* By ~ Xarah Bukar Washe gari An shaida daurin auren su akan sadaqi 100k nako wacce, baba shehu sai yaken dole yake, yaso ace abba ya hakura da batun Kursum, amma sai yazo mai da xancen hadasu auran da zee, ba yadda ya iya shiyasa ya nuna hakan ma daidai ne…jiki a sabule ya dawo gida, meerah da zee dake zaune a palo suna jiran good news suka tsorata ganin ya shigo fuska amurtuke, “zee tace baba lafiya dai koh ?? ko badani aka daura ba….ya nisa yace zainab sai dai kiyi hakuri, ku biyun aka daura masa, wat ta kwalalo ido diz cnt b possible, shifa ya yazid da bakin sa yace bazai aureta ba, hw cms ya canxa mind… baba shehu yace I don’t tink yazid yasani, danko daurin auren baije ba, it seems iyayen kawai suka san xancen, zee taja tsaki, am very sure uwarsa ta hada komai shegiar mata, aiko xanyi maganin ta….”indai kinason zaman lapia kuma danta ya soki dole ki girmamata, cox idan aka sakoki babu ruwana, namiki iya kokari na, ya haura sama abunshi Meerah tace calm down, auren bashi da amfani ai, tunda Kursum din na prison, ” idan tafi to fah ya kenan ?? ta kwashe da dariya, ai bazamu bari ta fito ba, zee tace bangane ba ?? meera tace ina da connection a prison din, kudi kawai zamu biya agama da ita, atsorace zee tace akasheta kenan ? kwarai kuwa, idan ta mutu kowa ya huta, zee tace idea din yayi amma it risky, bari musan yadda trial dinta zai kasance tukun, meerah tace toh let wait n c, yanxu muje ki kwashe kayanki, xan kira frnds dinmu suzo mu rakaki gidan miji dan banga alama abokan ango zasu zo ba, zee tayi dariya, wlh kaman kin sani, muje ki tayani hada kaya Kusan sau uku yana knocking kofan ba respond, ya murda yaji gam kofar a kulle, ya leke dakin gimbiya, ke hafsatu ina hajiya ? kota fita ne ? naga kofar ta rufe, gimbiya dake shafa mai ta juyo ayatseni tace hajiya bata nan, tun safe ta tafi zamfara ganin mai magani ciwon baya ita da samira, yace miyasa bata gayamin ba ? tace oho nasani, tacemin in gaya ma zata dade, ba saika naime taba, idan tayi settling zata kira ka….toh kawai yace, sam bai damu ba, dan zaman hajiya agidan bashi da amfani. Prison Yau sanitation tun safe suke gyare gyare, lady D na hakince kan kujera tana basu order, “kursum na daga gefe tayi tagumi, duniyar ta mata zafi, bata taba expecting ya yazid zai guje taba, gashi wani irin so da kaunar shi ke ruruwa cikin zuciyar ta, ” dukan da taji abayanta yasata dawo hayyacinta, a tsorace ta dago, Ta kare mata kallo, irin matan nan ne masu kirar maza, fuska bakikirin ba annuri, da kyar tace baiwar Allah lapia kika dakyan ?? Matar da ake kira da snake ta balla mata harara, koma waye ubanki we are all criminals anan, banga dalilin da zaisa muna aiki ke kina zaune kina kallon mu baaa… tasss kakkaywan mari da taji afuska ya hanata karasa wa, “rai abace lady tace how dare you touch my property….” tsum snake tayi, shikenan kashin ta ya bushe, baki na rawa tace lady am sorry bansani ba, lady ta kara wanke ta da mari, ba shiri ta duka kasa tana bada hakuri, lady tace next tym kika tabata am gonna cut off ur hands, ta kalli kursum, hop u are okay ?? akidime tace yes, dan ba karamin tsorata taiba akan cire hannu da xaai….”madam ta karaso wajan tace meke faruwa ne ? da sauri snake tace notin, we are just talking, tasan halin madam sarai tana iya kaifa solitary for 2weeks, madam tace okay, ta kalli kursum, maza kije waiting room, sm1 is dia to c yhu, “tace toh, da sauri tabar gun da murnan ta, tana patan Allah sa ya yazid ne yaxo, ” tana shiga taga barrister shu’aibu, suna gaisa tana binsa da kallon mamaki, yace kar kiyi mamaki, nine lawyer mai kareki…..”uhmm daka barni kawai, nida banda ko sisi biyanka.. ” yay murmushi, karki damu, yanxu gayamin dangartakar ku da sumy ? “ta nisa sannan tamai bayanin komai, yace toh shikenan, don’t bother urself, idan mun shiga court gimbiya da hajiya are d perfect witness to diz case, ” tamai kallon rashin fahimta, tace bangane ba, hajiya da bata kaunar ganina, how cms zatai testifying, mi zata ce ?? “yace i cnt say, amma kisani duk abunda zata ce shine zai ceceki, ” tayi shiru, itadai tasan babu wani good relationship tsakanin ta da ita, Allah kadai yasan abunda zatace, tace nagode sosai brstr, “yace karki godemin, hajiya zaki godewa, ya mike tsaya, ni xan wuce sai mun hadu a court, sukai sallama ya fice…..itama ta koma ciki a sanyaye.. Gidan shiru kaman ba buki ake ba, gaba daya yan’uwa sun tattara sun tafi, umma da abba ne kadai zaune a Palo suna hira kasa kasa, “yace kin nace ayi auran gashi anyi, miye kuma bakyaso yasani, ” kyale ni dashi kawai, so nake na nuna mai kuskuran sa, tunda ka zaba mai zee amatsayi mata ai shi kenan, “ya gyara hulan shi yace Allah ya kyauta, ya mike ya fice.. ” yazid ya shigo fuska amurtuke ya zauna, umma ina wuni ?? “ta amsa lapia, fuska daure ” yace yanxu umma abunda abba yayi ya dace, ya xaai ya daurin min daure da zee, dat gal is crazy, “umma ta balla mai harara, I tot kace kana iya auran kowa ya zaba ma, miye kuma kake complain, kaje ka zauna da zee tunda ita abba keso…” Xai kara magana tayi saurin taran numfashin sa, ya isheni haka, kamin shiru kawai “yay shiru, yarasa laifin da yayi umma ke fushi dashi, daga bisani ya mike yaje daki ya zaune.. Ganin yammata kusan su hudu na shigo da akwatuna, yasa ta mike tsaye ta kare masu kallo, tace Ku kuma daga ina babu ko sallama zaku shigo min gida har cikin Palo ?? daya daga cikin su tace amarya muka kawo…”umma tace lailai kam wace marar kunya amarya ce daku zaku kawota?? “Ni CE nan, ta shigo tana rangwada, meerah tace umma munzo siyan baki, ina mijin yake ne ? ” haushi da takaici ya hana umma cewa uffan, tadau wayanta ta shige daki… zee tace woww, Ku zauna plz feel at home, barin kawo mana drinks, suka zazzauna suna shewa, ta dauko tabasu, suka baje suna hirarsu ta batsa, ba kunya ba tsoron Allah, meerah tace galfrnd ina yake bangan shiba,tace I tink yana daki, barin je insa meshi, “eh kije, kinsan lallaba shi zakiyi har ya tsaki jiki, tace toh, da sauri taja akwati ta wuce dakin shi…. Yana zaune ya kafawa waya ido, ahankali nima na leka, ba komai yake kalla ba face picture dinta daya daura a screen saver, ta turo kofa ta shigo, ya dago sukai 4eyes, ” rai abace yace ke kuma fah ,miye na shigo min daki harda tarkace ?? “ta karaso gabanshi tace haba baby am now ur wife, kuma kasan gatan mace dakin mijin ta, ” yay banza da ita… my love say sumtn mana, kayi shuru….ta matso dab dashi zata shafa mai fuska, da sauri ya mike akufule, karki kuskura ki tabani, just stay away from me…fuuuu ya fice, “taja uban tsaki, ta dau wayansa taga ashe pic din Kursum yasawa ido, lailai har yanxu yana sonta kenan, aiko zata dau mataki tun kafin ma yasan an aura masa ita… Wani kololon bakin ciki yaji ganin su a Palo sai hauka suke, “ya daka masu tsawa, ba shiri suka kintsu, yace koku bar gidan nan ko yanxu yan’sanda suzo su tafi daku, caraf meerah tace haba yaya mi yayi zafi haka, we are just leaving, ta kalli sauran let go, suka mike tsum tsum suka fice, ” yaja tsaki yace wace irin rayuwa ce wanan ( idan ka tambayeni in tambayi wa:?) yadau mokullin mota ya fice daga gidan……”ta sauko tana cika tana batsewa, taga ba kowa Palo tace badai sun tafi ba, ta leka kitchen taga inna zaune da hanifa tana bata abinci, taja tsaki, ta karasa ta dauke hanifa, ke tsohuwa nice uwar hanifa yanxu, so ki tattara ki koma kauyen da kika fito, “inna tace yarinya ba saikin zageni ba, zan tafi, amma kiji tsoron Allah idan kika zalinci hanifa zaki hadu da hukuncin ubangiji, ” zee tace naji, ki tafi kawai mun hutar sheki, “barin shiga enma umma sallama, ” ta wurga mata harara, babu inda zaki, daga nan gate zaki wuce straight, “toh kawai inna tace tadau gyalanta tabar gidan…. Bayan kwan biu Federal high court 11.45am Duk sun hallara ana jiran karaso wan alkali, ko wanne su da mugun abunda yake ainawa cikin zuciya sa, banda salma da huzaifa da sukai shiru suna jira suga kursum, salma tace yaya kana ganin xaa dace kuwa, yanda nake ganin su baba shehu ko ajikin su, “yace kalesu, ta Allah ba tasu ba….” meerah dake Zaune ta baya, ta tabo zee tace babe hw far na, ya yazid baze zoba ?? “I don’t tink zai zo, nifa ko magana bayamin, ya hanani zuwa kusa dashi, ” kai haba dai, kice ko first nyt baku yiba, “uhmm shida ko kallo na baiyi balle ma ayi harka, idan nayi kokarin cusa kaina tashi yake yabar min bed din, ita kuma umma bana ma ganinta, she is alwayz indoors, meerah tace gaskia baya da mutunci, zamuyi maganin shi.. ” Gaskia munyi dabara fah, yanxu dai zamuga waxai ceceta, gimbiya ta murmusa, kedai bari, ai suda ganin hajiya har abada, saidai Kursum ta fada duniya, babu mai tallafa mata, “hinde tace aiko dai, naga shehu sai fara’a yake…” kyaleni dashi, nariga nayi planing abunda zan mai, bari agama da yarinyan nan tukun.. Barrister shu’aibu ne zaune, ya duba tym, yay tsaki, yakamata ace hajiya ta zo, ga line dinta switch off, da sauri ya fita wuje ya kira layin umma, tana gani ta dauka da sauri… “Hello barrister har kun gama ne, ” yace yanxu dai xaa fara, hajiya shuru bata zoba… “tace haba dai, kodai mantawa tayi, barin tura huzaifa yanxu nan yaje ya dauko ta, ta kaste kusan minti biyu huzaifa ya fito da hanzari shi, brstr yace karka dade plz, ita kawai muke jira, ” yace yanxu kuwa, yaja mota da sauri ya wuce.. yana komawa ciki, alkali harya shigo ya zauna, yan’sanda suka shigo da Kursum, duk suka bita da ido, zee taja tsaki, tana prison amma she still looks good.. Alkali ya kalli papers dake gabanshi sannan ya dago yace the defendant is accused of I.d, fraud & kidnapping and plead innocence, “prosecutor yace haka ne, ina so court taban dama in mata tambayoyi, alkali yace an baka, ” ya karaso gaban ta yace muna iya sanin cikakken sunanki, ta fada agajarce, dan tsayuwar ta fara isarta, yace miye hujjarki na kidnapping yarinya bayan kinsa itace ya kamata ta gaji makudan dukiyar da kakanta yabari amma ke kika gaje alhalin baki hada komai da ita da, caraf brrst shu’aibu yace objectn my Lord, tambayoyin nan basu dace da shariar nan ba, alkali yace objectn sustain, kidnapping case is dismissed tunda actual family din basuyi pressing charges ba, prosecutor yace toh inaso Alhaji shehu fito ya bada sheda akan yadda tayi running company din 4 almost a year, “baba ya Mike da sauri ya karasa witness stand, prosecutor yace ya lamarin company ya kasance tun lokacin da ta maye gurbin shugaba ?? ” ya nisa, gaskia tunda tazo komai ya tsaya cak, ga makudan kudade an naima an rasa, kusan wata hudu baa biya workers ba, prosecutor ya kalleta, ina kika boye kudaden da aka rasa, ko kina da foreign account inda kike tarasu ??? tayi tsuro da ido, aranta tana mamakin karya irin na baba shehu, dakyar tace ban boye komai ba, kuma bani da labarin missing kudade, “ya kalli alkali yace nagama tambayoyi na, brrst shu’aibu ya mike tsaye, ko hajiya hafsatu zata iya fitowa, tsum gimbiya ta mike, tazo stand, yace munsan ke kika rainasu tun suna yara, kina iya bamu kataican can tahiri akan dangartakar wace ake tuhuma da marigayiya ?? ” kwarai kuwa nice amatsayin uwarsu basu da kowa agarin saini, tun asali Kursum bata da aminiya data wuce sumy, kowa yasan su tare, amma dayake Kursum akwai hassada da kwadayin abun duniya, shiyasa sumy ta rabu da ita, dan randa zasu tayi kano har office sumy tazo tasami tace koda ta mutu Kursum CE ta kashe ta, dan tana yawan threatening dinta akan idan bata bari taje gidan su ba……daga brrst har kursum tsakin baki sukai jin makircin da gimbiya ke kullawa, brrst yace waye shaden ki lokacin da tazo office dinki ta gayamaki ??? “tayi shiru, prosecutor yay objecting, alkali yaba shi dama, ” ya karaso gaban gimbiya, yace kinsan cewa wace ake tuhuma ta saci rayuwar mai rasuwa, miyasa kikai shuru baki gayawa kowa ba, kenan kema u are her accomplice, “gimbiya tace cemin tayi zata kasheni idan na tona, shiyasa nayi shuru da bakina, ” yace toh, kina iya komawa ki zauna.. Duk ya kideme banda zufa ba abunda yake, bai yi tunanin haka case din xaiyi zafi ba, ga har yanxu hajiya basu zo ba, ya kalli alkali, inaso court taban minti goma kacal har main witnesses din ta karaso, “alkali yace baa haka a court, every1 is expected to be here, tun kafin in shigo, amma nabaku minti 5 kacal…. Kusan minti biu shuru, babu ma alaman su, gashi ba daman making call, gimbiya sai fadada murmushin ta take, minti biyar na cika, alkali ya buga tambari yace since d defense witnesses is not here to testify, d defendant is declared guilty……:oops::oops: *Xarah Abubakar* *Dedicated to Badia sallau* ~luv u ol~ [04/10 6:12 AM] : *KURSUM* By ~ Xarah Bukar Kana nufyn ba kowa agidan ?? “mai gadi yace tabbas ba kowa, da zasu fita sukace arufy ko eena ” hajiya bata ciki ne ?? yace eh bata nan, alhaji shehu yacemin tayi tafiya kwanaki biu da suka wuce, “okay tau nagode, ya koma mota, ya fiddo waya yay dialing no din umma, bugu daya ta dauka.. ” huzaifa ya ake ciki ? kasa mae ta? “ya nisa yace umma akwai matsala, hajiya bata gari, sunce tayi tafia…”tayi shiru, daga bisani tace toh shikenan ka koma court, xan cigaba da trying line dinta, yace okay, sukya sallama… ” jiki asanyaye ta ejiye wayan, tana mamakin ina hajiya taje alhalin tasan yau ne trial din, gaskia sumtn is fishy ba yadda xaai ace bata nan, amma zata bincika dai.. Court Duk sun girgiza da kalaman alkali, banda mutane hudu da suka kara fada’da fara’ar su, “alkali ya cigaba da magana, due to rashin hujjoji masu karfi, wace ake tuhuma ya zama dole tayi zaman kurkuku na wata uku….” dumm gaban kursum ya fadi, dagowa tayi ta karewa gimbiya da baba shehu kallo mai dauke da tsana, tasan sarai sune suka ja mata kuma ta tabbata harda hadin bakin hajiya, brrst shu’aibu ya karaso wajanta yace kwantar da hankalinki, nasan uxuri ya hana hajiya xuwa, muna da daman kara bude case din anytym, idan har taxo tayi testifying u are save, “ta kalle shi da idanuwa ta dasuka sauya launi zuwa ja tace indai hajiya ce xata taimake ni banaso, na gwamma ce inyi spending life dina a prison, ka gaya mata I don’t need her help, infact i hate her…” xai kara magana yan’sanda suka wuce da ita…. “gimbiya taja tsaki, ya xaai alkali ya bata 3months kacal, muda muke expecting 20years,” hinde tace lailai we have to strike fast, cox idan ta fito prison kashin mu ya bushe, “kedai bari ai banga ta xama ba, cikin wata ukun nan xan cika burina in waske, bazaku kara gani na ba, ” hinde ta balla mata harara, kardai ki manta idan kudin sun samu 50-50 zamuyi, “eh mana tawan raba dede xaai….” baba shehu ko ajikin shi, sam bai damu ba, yasan kota pito prison bazata doso gidan ba.. Gaskia we have to do sumtym, dan baxan yadda ta fito so soon ba, am very sure har yanxu ya yazid nasonta, idan ta fito am finished, “meerah dake saura ranta tace calm down, miye kike tada hankali akan minor abu, nariga na mana planning komai, today will be her last day on earth ” zee tace bangane ba, wana plans kikai ??? “ta kwashe da dariya, akwai wata prisoner da guy dina ya hadani da ita, naje munyi magana na nuna mata pic din kursum, ita nakeso akashe koda ta dawo prison din, kinsan mi tace da taga pic din… ” a’a gaya min….”cewa tayi itama she has been targeting her, cox akan kursum sai da tarasa ido daya tsananin marin da wata tai mata.. “Zee tayi murmushi tace galfrnd u are rily smart, killing her is d best option, amma ya sunan prisoner din ??? ” I dunno her real name, nasan dai ana kiran ta da Snake ……. *Xarah Abubakar*:) *Dedicated to Badia* ~luv u oll~ *KURSUM* By ~ Xarah Bukar kara k’cewa da daria sukai daga bisani suka tashi suka fice, ta ajiye meerah agida sannan itama ta wuce gida “abba da umma na dinning suna lunch, ta shigo ayatsine, ko kallan su batai ba ta wuce daki, ” umma ta nisa, kaga halinta ko, sam batasan darajan mutane baa….”hannu abba ya daka yace dakata plz, ya kamata kina mata uzuri na tabbata bata lura damu ba, uhmm umma tayi tai shuru “qwas!! qwas!! ta dawo Palon, suka bita da ido ….ta karasa dinning ta zauna tare da binsu da kallon banxa tace ina husby na ban gan shi ba….” dakyar abba yace baya nan na tura shi wani aiki abuja da safyn nan, bai gayamiki bane ?? “tace kaii matsala ta da tsappi kenan, sai bakar munafunci, ya’xaai ya gayamin tunda uwarsa naima kai take dani, ” akufule abba ya kalleta, kina da hankali kuwa, mu kike zagi ?? “taja tsaki tare da mikewa tsaya, kudai ku kasani, tafiya ta xanyi idan yadawo kwa ganni, fuuuu ta fice….” umma ta girgiza kai,uhmm yaudai ka gani da idonka tun baa je ko ina ba, yace lailai kam nagani, amma kyaleta kawai, taci darajan amintakar dake tsakani na da marigayi alhaji tanimu dayau na raba auran nan, “aranta tace Allah sarki, ita kursum da baka kauna ba kasan itace diyar saba, afili tace sai hakuri, yaran yanxu sai fatan shiriya….Amin kawai yace yay shuru dan ba karamin shaka yay ba.. ” umma tace “munyi magana da huzaifa, akan mi ?? ya tambaya….akan kursum, wata uku xatai a akurkuku, ka taimaka kabarni in dubota ko sau dayane, ga hanifa sam bata da sukuni rashin ganin uwarta, “yace toh naji amma ba yanxu ba… Abuja Zaune yake a hotel din daya sauka ya bude suitcase dinshi ya ciro wasu papers yana duba wa, yaci karo da dairy dinta, ya bude first page, ba wani rubutu masu yawa bane, ya karanta: ” I liked yhu from d first moment I saw u, when I declared ur love I kept it in my mind cox it was one of the happiest dayx of my life, dou yhu came to me to brighten my life, tanks to u I knw wat to be truly loved it is. All d words in the world are not enough to tell yhu……I love u so much yaya yazid, “I hope one day u will find a place in ur heart to 4give me of all my mistakes……. “Jikin shi yay sanyin, ya rufe da sauri ya ijiye, yace anya banyi kuskure ba, yay saurin kawar da tunanin, ya duba fone dinshi yaga 10missed calls na zee, tsaki yaja ya kashe wayar, aikin sati biu yakawo shi amma sai ya cika wata guda kafin ya koma, ya mike tare da kwashe papers din ya wuce office Kano Kinyi daidai da kika baro gidan kika dawo nan, dan kin damu dashi datx y yake miki bura ubar daya ga dama, tsabagn askanci da rainin wayo yasan xaiyi tapia shine bai gayamaki ba, “zee dake zaune ciki da takaici tace kedai bari, ai harda hadin bakin iyayan, Sam basu dauke ni da daraja ba, meerah tace shiyasa nace ki rabu da yazid basonki yake ba, atleast choose sumtn good in ur life, ga olamide tun muna skull yake bibbiyar ki kinki kula shi, yanxu haka ya shigo kano, yana ma hanya zuwa nan ” kina nufin na ajiye aurena aside in kula shi kenan ?? “a’a, auranki na nan mana, zafi kawai zaki rage tunda shi mijin is not ready…..” zata kara magana suka ji knocking door…..meerah ta tashi ta bude, da fara’arta tace olamide long time, “yayi dariya ya karaso ciki, ganin xee zaune tayi kicin kicin yasa shi kara darawa yace my love baza kiyi wlcmn dina ba, ” harara ta wurga mai taja tsaki, ita dai baya burge ta Sam….”meerah tace don’t mind her, zauna barin kawo mana solution, ta shiga daki ta kwasa masu giya kusan kwalba takwas ta diri masu, ola yace wow kinsa na tuno da scul yadda muke baje wa asha ayi tatil, “hhh aifa dole mutum yay enjoying life kafin ya tsofe, ” tsaki zee ta kuma ja sannan tadau bottle daya tafara kwankwada, ola ya dan saci kallonta yana murmushi Akufule ya kalleta, ashe baki da hankali, kujerar M.D danai shekara da shekaru ina naima, yanxu nasamu shine zaki xo min da xancen banxa wai kema m.D din kikeso, ke asuwa ?? toh wlh baki isa ba….”tayi shewa tace shehu baa ja dani, ko ka bani m.D ko kuma in tona asiri kai kasa nawa kursum shairi, “ya kwashe da dariya, kinyi blackmailing dina d first tym na kyaleki, diz tym saidai kiyi abunda xakiyi cox it won’t work, infact zaman ki gidan nan it over, pack ur tinxx n leave ” gimbiya tayi tsuro, tabbas inta biye mai xai iya wurgi da ita, ta marairace fuska tace haba shehu mai yayi zafi haka, kayi hakuri wasa fa nake….”ya wurga mata harara, nidai ina baki warning, if yhu try anytn stupid jikin ki xai gaya maki…”yaken dole tayi tace toh, ta koma dakinta rai bace.. “hinde dake zaune ta taso da sauri, lapia dai koh ?? ta kara tamke fuska tace nayi iya kokari na I don’t tink xai bada hadin, hinde tace akwai matsala kenan, ” kwarai kuwa, xan kyale shi 4 now, sai komai yayi sanyi zamu mai d hard way… Prison 1.46am Dare ya tsula wasu har sun kwanta, banda kursum dake zaune cell din lady suna hira, “lady da akema kitso tace it seems gimbiya nan bakin su daya da baba shehu datx y suka hada baki wajan miki karya, ” kursum tace nasan halin gimbiya, she cnt be trusted, am sure tana da wani hidden plans akan shi, “Lady tayi kwafa, ai wasu akan kudi dey can do n undo.. Ta tabo mai mata kitso, ke maza ceki laundry room ki dauko min towel dina, tace toh…..” Kursum tayi caraf tace a’a ku cigaba da kitson barin je in dauko, lady tace okay b carefully “Hankali kwance ta mike ta fito, tana tafe wani shadow na binta, sam bata lura ba, ta shiga ta dau towel din, xata fito kenan taji an shake mata wuya tabaya tare da toshe mata baki, atsorace ta kwalalo ido, tana kokarin magana takasa….. ” ganin shadow din zungureren wuka yasata gigicewa……. *Xarah Abubakar* *Dedicated to Badia* Xarah’s Novel [04/10 6:13 AM] : [03/10 9:16 pm] Xarah : *KURSUM* By ~ xarah bukar Dakyar ta kwace kanta tana hakyy, ta juyo agigice, ganin snake rike da xungureriya wuka fuskar ba annuri yasata kara kidi mewa, “snake tayi yake ta karaso tab da ita ta matse ta a bango tace ko kinyi ihu bamai ji balle ki xata xaa ceceki, daga ni sai ke…kiyi hakuri ki kyaleni plz….ta hauta da kakkyawan maruka ta ko wana angle a fuska, baki har yana zubda jini, “Baki na rawa Kursum tace antee snake dan Allah karki kashe ni kiyi hakuri ki kyaleni plz….” hhh tunda kin shigo hannu dole kibi ancestors, ta dago wukan zata caka mata suka ji anturo kofa an shigo, atsorace tayi wurgi da wukan ganin lady tsaye ba annuri tare da prisoners guda uku.. “aguje Kursum ta karaso gurunta tana kuka, ta kalli fuskan ta dayay ja ga jini na xuba ta hanci da baki, tace pretty who did this ?? kasa magana tayi, saima kukan dayaci karfinta…..” Ran lady ya baci matuka, ta karasa wajan snake datai tsuru tsuru gabanta na dukan uku-uku, ta shakota, dint I warn yhu to stay away from my property, “murya na rawa tace ba lafina bane I was just following orders, ta kara tamke ta, orders 4rm who ?? ….uhmm I dunno knw her name, munyi da ita kawai zata biyani idan nakashe pretty…” Lady tace datx good, ta kira daya daga cikin guards dinta tace bani wukan nan, ta mika mata, oya Ku rike min ita gam ku bani hannuta “akidime snake tace mi xaku min ?? lady tace alkawarina xan cika, ta dauki kayan dake wajan ta daure mata baki tamau sannan tasa wuka ta kille mata two fingers kattt kattt ….:oops::oops:ba snake kadai ba hatta Kursum dake gefe saida ta tsorata ga jini sai tsiyaya yake ” snake dan azaba sai mukursusu take tana zubda hawaye, ga baki an tamke balle tayi ihu kotaji dan dadi…”lady tace kadan namiki yanxu buh next tym am gonna cut off ur head, ta kalli guards din tace ku gyaran wajan sannan ku kaikai ta clinic ayi treating dinta, ke kuma ta nuna snake da yatsa idan an tambaya hw cms, cewa zakiyi u had an accident wen closing d doors.. “Da sauri snake ta daga kai tace yes, I had a terrible accident, ” tayi murmushi tare da ja mata cheeks, yauwa good gal ashe kingane……taja hannu Kursum suka bar wajan Suna zaune tana goge mata fuska tace acikin su wa kike ganin ya bada order akashe ki, dan yadda snake tayi magana am sure mace ce, “Kursum ta sauke dogon ajiyar zuciya, I dunno, amma ina suspecting mutum uku, gimbiya, zee ko hajiya, ” lady tace I don’t tink hajiya nada wani motives akanki, tunda kince ba wani cikakken lapia gareta ba, ni aganina zee ce cox ita keda reason din kawar dake, tace hakane fah, koma dai miye Allah ya fisu, tankx to yhu am alive Da safe 10.42am Farkawa tayi tare da mika, ta yunkuro xata tashi taji wani irin azababben ciwo tsakanin cinyoyinta, ta dube jikin ta dako kaya babu , afirgice ta daga com4ta data rufa dashi takara tsorata ganin aika aikan daya wanxu, ta duba gefe, yana bacci hankali kwance, ta daddage ta daka mai duka, tsum ya tashi akufule….miye haka ?? “a hasale tace ola wat did u do ?? yay dariya, excuse me wat we did zaki ce, kokin manta ne….” tayi shiru tana son tuna abunda ya faru, ita dai tasan last nyt she was drunk, amma ina meerah take ? hw cms na dawo daki ?? “ta kalle shi araunane, I cnt biliv u took advantage of me…..yace my love kar kice haka plz, u knw I love u…” ta wurga mai harara, yhu stole mah virginity, I hate u n I’ll neva 4give yhu….ya matso xai tabata, tayi ihu tare da wurga mai pillow, don’t u dare touch me, infact i dnt want 2 c ur face again, just pack ur tinxx n leave….”yay shuru yana kallon ta daga bisani ya tashi yasa kayansa ya fice “Meerah ta shigo da saurinta, zee miya faru naga ola ya fita rai bace, ” ta harareta, don’t play dumb ai kinsan abun da ya faru, tace ohh nikam bansan Komai… “kar kimin karya just tell me wat happen last nyt…..ta nisa tace nima I cnt recall nasan dai we wia all drunk, bansan hw cms kuma keda ola kuka fara smooches, ni kuma daga nan I slept off… ” ta buga uban tsaki, wlh ya cuceni, I wantd mah husby to be my first, amma shegen nan yaxo yamin basaja, “meerah tace calm down, miye aciki atleast yanxu kin zama big gurl, ni yanxu fita xanyi amma barin hada miki hot ruwa ki gasa jiki….Ina zaki ?? “tace xanje ganin snake ne, kinsan ya kamata musan kota cika aiki, zee tace gaskia ne Allah sa a samu good news, ” ta kece da dariya, don’t worry, just chill up, yanxu xanje in dawo… Prison Kursum ce zaune da inna a visitors space, inna tace munyi waya da umma ta na gaida ki, hidima ya hanata xuwa, tana samun lokaci zata zo…..”tace ba komai ma, umma ta nuna min kauna saidai Allah ya saka kawai. “ya akai fuskan kin kumbure, an miki duka ne ?? “tai murmushi, ba komai fah bugewa kawai nayi, ya hanifa?? Inna ta numfasa tace uhmm tana nan kalau, nida uwarta tamin rashin M, ta koreni daga gidan…” kwalalo ido tayi tace wace uwar ?? “Zainab mana, matar yazid din…agigice tace sunyi aure ne….” eh mana, ai baa daga auran ba, da ita akai…..innalillahi wa inna’ilaihi raji’un ta furta a tsoroce, tace shi kenan inna kashe min hanifa xatai….”karki damu baa abunda ta iya tunda umma na nan, mudai fatan mu ki fito lapia, “jiki asanyaye tace nifa kona fito banda gidan zuwa, inna tace ahab gida ba matsala bane, kinga ni gobe xan koma bauchi, xan iya bar miki mukullin gidan da nake, saiki yi zaman ki can….” nagode sosai inna, gaskia kin kyauta min, Allah yabar zumunci, tace ba komai wlh, nima kin taimaka min lokacin da babu.. “Murmushi Kursum tai,tayi shiru tana mamakin irin kiyayyan da ya yazid ke mata, koma dai minene tasan ita yakeso ba zee ba, zata bashi tym harya huce Suka cigaba da hira daga bisani inna tai mata sallama ta tafi…. Ta tashi ta koma ciki asanyaye, sukayi kicibis da snake zata shiga V.s, ta kalli hannuta daya sha bandage abun tausayi, da sauri taja gefe taba kursum hanya ta wuce, dan ba karamin tsorata tai ba….” ta karasa v.s ta zauna, meerah dake jiranta ta kalleta ayatsine, ke kuma lapia naga hannu daure ?? “Snake tace ke aiki bai yuyuba fah cox sum1 is protecting her, yanxu haka saboda ita nayi loosing two fingers…..” ta kwashe da dariya, u’r so stupid, dan aikin nan kika kasa, mtsww “snake tace don’t insult, xan baki contact din bro dina ki bashi kudin aiki…..” ta balla mata harara, ai babu balance tsakani na dake, wana aiki kikamin ??? “tace ban miki aiki ba,amma akan aikin komai ya dawo kaina, dan haka u must give me sumtn….. meerah tace u are not serious, ko anini baki samu, kinga tafia ta, ta mike tsaye ta wuce abunta….” snake dake zaune rai abace ta mike ta koma ciki, aranta tayi alwashin daukar fansa akan meerah komin daran dadewa….(hhhh ) *Bayan wata Daya* Gimbiya da baba shehu an shirya kaman gaske, suna kan dining suna breakfast, baba shehu yace wai hajiya bata kira ki bane…”tace eh jiya ta kirani tana gaida ka, inda sukene ba network mai kyau….”yace no wonder bana samunta idan nakira, “e wlh, nan da wata uku ko hudu zata dawo…ya nisa yace Allah sa dai lapia, dadewar tayi yawa, nizan wuce office idan tasake kira kice ta naime ni….” gimbiya tace toh aranta tace saidai wata ta kira badai itaba:twisted::twisted: Umma ce tsaye a daki ta goya hanifa dake kukan bacci, kusan wata daya kenan tana cigiyar hajiya ba labari, ance taje zamfara har yanxu shuru bata dawo, har gidan taje aka hanata shiga wai gimbiya tasa doka kar ashiga, “taji wayanta na ringing, ta duba taga yazid ne, da sauri ta dauka… ” suka gaisa lapia lau, dan yanxu ta rage fushi, tace my son ya kamata dai ka dawo, I miss u alot..”yace gobe xan dawo umma, ya hanifa, hop dai zee na kula da ita….tace uhmm hanifa is fyn, matar ka kuma banda case da ita, so karma ka tambaye ni ita, “yace sorry my umma, ya labarin kursum ?? tace ina ruwanka da ita, I tot u said she ix dead to yhu…” Just asking kawai, tace don’t ask plz, kuma ka tabbata ka dawo gobe, ta katse wayan…… “yay shuru yana kallon wayan, umma CE kawai yasan tasan labarin ta, ya sauke ajiyan zuciya, yace tabbas salma zata sani, ya duba contact babu no dinta, yay tsaki, da kunya kuma ya kira huzaifa ya tambaye shi…..haka dai ya zauna shiru asukwane Suna zaune Doctor ya shigo da result, ya kalli zee data fita hayyacinta kwana biu yace congrat madam u’r one month pregnant, meerah tace haba dai doc kodai result din wata ne, yace a’a, yamika mata paper,karanta da kanki….ta duba, ta tabo xee ke dagaske nefa….”akufule zee ta tashi tayi waje, gaba daya hankalinta ya tashi, ” meerah ta biyo ta aguje tana kiranta, tayi banza da ita…suka shiga mota, taja afusace, “galfrnd take it easy mana, so kike muyi accident ne, ” dakyar xee ta iya cewa kyaleni kawai inada unfinish bizness da Kursum, tunda bata mutuba I have to try sumtn new…..”tace okay oooo, nidai xan jiraki a mota….. Suna isa tayi parking agurguje, ta shiga da sauri ta…… Tana zaune security guard yaxo kiranta tayi bakuwa, ta fita zuwa v.s tana mamakin ko waye, kusan wata daya kenan ba Wanda yaxo……tana zuwa taga zee CE,tace sis yau kin tuno dani ne, “ta wurga mata harara, nazo baki warning, koda kin fito karki kuskura kice zaki nemi ya yazid, dan yanxu haka ina dauke da cikinsa na wata daya…..plz ina rokanki stay away from us, yadda hanifa bata rayu da uwarta ba karki sa dan cikina ya rayu ba da uban saba, ki taimaka plz……ko jiran amsan Kursum batai ba, ta juya ta fice……itama kasa tashi tayi banda zubda hawaye da take, wato ya yazid har ya manta da ita so soon, tayi alkawarin hakura dashi koda sonshi xai kasheta…. Ba wanda yace uffan har suka dawo gida, suka zauna Palo shiru daga bisani meerah tace waike xee miye haka, kinyi shuru tun dazu, ta nisa tace mi xance toh…diiinn taji karar msg ya shigo wayanta, ta duba, msg ne daga ya yazid, da sauri ta karanta….”ta dago agigice ta kalli meerah, oh my God ya yazid is coming baq 2moa , tace toh sai mi dan xai dawo, “akidime zee tace na shiga uku,INA dauke da cikin olamide taya xan koma gida…..” tace abu mai sauki ayi aborting kawai….caraf akunnen ola dake tsaya bakin kofa yana shirin shigowa…..ya karaso yace babu wanda xai kashe min DA Ina Raye……. “atsorace suka juyo suna kallon shi:oops::oops::oops: *Xarah Abubakar* Xarah’s Novel kursum 71 to End Posted by XARAH ABUBAKAR on NOVEMBER 13, 2016 [08/10 6:49 pm] cute xarah : *KURSUM* By ~ xarah bukær Ta kalle shi a yatsine sannan tace kwarai kuwa zubda cikin xanyi, dan baxan yadda na haifo shege ba, “ya sauke dogon ajiyan xuciya, araunane yace plz zee don’t abort my child, nasan u hate me buh plz don’t kill an innocent soul…… ” tsaki ta bugu tare da gyara xama, “meerah tace galfrnd I tink he is ryt, kuma kinsan xubda ciki is very risky xai iya causing life dinki.. ” atsorace ta mike tsaye tana girgiza kai, gaskia m not ready to die, xanbar cikin but on 1 condition.. “wat condition?? ya tambaya atakaice ” stay away from 4rm me, nayi alkwarin idan na haihu xan damka maka babyn ka coz am not ready to b a mum, “yakye yayi tare da sosa keya, yace okay na yadda, ya kalli meerah, plz ki kulan mu dasu…”tai dariya tace ai dole, abu namu… yay murmushi ya fice. Meerah tace aiba xama xakiyi ba, tashi xakie ki koma gida, karya dawo ya riske baki nan,”ta numfasa sannan tace bansan ya xanyi ba, abunda bamu taba yiba balle ince cikin na shine, “abu mai sauki kiyi kokari ayi harka kawai, dan ki samu lakamai shegen…tace I have try dat for so long, still ba hope:|narasa ya xanyi, “just try again, maybe adace diz tym….uhmm xee tayi batace komai ba, can tayi murmushi tace galfrnd kina da pills nasa bacci ?? ” pills kuma ?? mi zakiyi dashi ? “Kedai bani kawai idan kina da…..” meera tace yea akwai, saidai yana da karfi sosai, infact idan kika sha bazaki iya tuna anytn daya faru dake ba a awanni goma da suka wuce, “zee ta kwashe da dariya, exactly abunda nake naima kenan, plz dauko min xan tafi gida yanxu, ” ta shiga daki ta dauko taba ta, da sauri ta Mike ta wuce gida. Zaune suke palo suna kallon 9pm news, ta shigo atsanake ta karasa wajan su, tace umma da abba ina wuni ? umma ta kalleta da mamaki dan yau ne rana ta farko data masu gaisuwar arziki, lapia kawai tace….”abba yace ya baban naku ? dumm gaban taya buga, wen last data ganshi ma, asali mantawa take dashi, dakyar tace yana nan kalau, tayi wuf ta shige daki dan tsayuwar tafara gaga ranta. “Umma tace anya yarinyan nan is alright, duk naga ta fige ta lalace sannan wanna change of attitude din bangane ba ?? ” wat du yhu xpect, yazid ya barta for a month ai dole ta shiga tashin hankali….tace aida tasan darajar auran da bata bar gidan ba, “koma miye su suka sani, yay shiru yacigaba da kallon TV Washe Gari Kin fiya xolaya nikam banga kyau dana kara ba, xaman kadaici ma ya isheni,”dariya salma tayi tace dagaske nake fah, nan da 2months baza mu gane kiba:) …..” kursum tace kedai bari aina kosa wata biu su cika, inbar yarin nan, danma inada good frndz masu kula dani, “salma ta murmusa tace matar ya yazid kice dai murna kike zaki ganshi ” kallon rashin fahimta tama salma, bangane ba wace matar ?? salma ta balla mata harara,kina nufin bakisan an daura muku aure ba?? nikam bansani ba, nasan dai zee ce matar sa…”Kema matar ce ai, ya huzaifa ke gayamin, ku biu aka daura masa…”tofah gaskia na haukari dashi, taya xaai zee data tsaneni ta xama kishiyata, ohh no wonder tace i shuld stay away 4rm dem…”salma tace aiko idan kika hakuri dashi kinyi loosing …”ya xanyi toh, shifa bayaso na yanxu.. “Yana sonki sosai, fushi yake, ki bashi tym xai sauko….uhmm I hop so.. Hankali kwance yake driving harya iso gidan, “zee na goye da hanifa a Palo, ya shigo fuska ba yabo ba fallasa, tana ganin shi tazo dasauri ta rungume shi, baby I miss yhu alot, ta kara makale shi tsam, yadan janye jikinshi dakyar yace easy karki sa hanifa ta tashi, ina su umma?? ” tace tana daki, ya raba ta gefe ya wuce….ta bugu uban tsaki tare da kwantar da hanifa kan sofa, dama dan taji shigowar shi yasa ta goyata, taje kitchen ta bude fridge ta dauko cucumber juice data hadamai, ta jijjiga dakyau sannan tayi murmushi ganin pills din data xuba ya narke. Umma ce zaune tana jan carbi, ya shigo tare da sallama ya zauna bakin gado, kusan minti 10 sannan ta i’da, “ta dago ta kalle shi, ” ya gaida ta, ta amsa da fara’arta tace yau kuma shigar dare ka mana ?? yay dariya, ya duba time yace yanxu fah 9pm yayi….”ta murmusa, ina fatan dai xaza dauki matar ka ku koma can gidanka, nagaji da sharing gidana, “yace umma kin gaji da ganina kenan ? ” a’a son kasan I love u alot, nan da 2month Kursum xata fito daga prison, na riga nagama arrangement nan zata dawo da xama datx y nakeso ku tattara…. “yace dama oll diz while tana prison ne ??? dan haushi tambayar kasa cemai uffan tayi….ya nisa yace wana prison take ?? tace I dunno, ” okay kawai yace, suka dan taba hira daga bisani ya tashi ya koma daki. Wanka yayi ya fito daure da towel ya zauna bakin gado yana danna waya, ta shigo sanye da hot sexy nyt wear rike da juice din ahannu, “kallo daya yay mata ya dauke kai, ta matso dab dashi tace baby ga best drink dinka na hadama…” gajerar tsaki yaja yace tnkxx na koshi “Ta marairece fuska, ya yazid narasa miyasa kake treating dina lyk no1, burina bai wuce in faranta ma ba, ga hanif kullum nike kula da ita, amma Sam baka damu dani ba, ” yay banxa da ita” “Ta fashe da kuka, baby plz say sumtn plz…. ” ya dago ya kalleta, karo na farko daya ji tausayinta, ta, ya jawota jikin sa yace banason kuka nan, mi kikeso yanxu ?? ta mika mai juice, tace idan kasha I’ll b happy cox I made it special 4 yhu, “yay murmushi ya karba yasha…” wani irin dadi taji tare da lumshe ido, ta kara shige wa jikin sa tana shafa mai kirji, “kasala yaji lokaci guda, idanuwan sa sunyi nauyi, starz kawai yake gani, “ganin yanayin sa yasa ta mike da sauri ta kwantar dashi ta kashe light ta cire kaya ta kwanto jikin sa tay lamooo…. “10.37am fone dinshi yay ta ringing, ” ta tashi da sauri tare fashewa da kuka, tahau kiran sa tana bubbuga shi, “firgigit ya farka yana karewa dakin kallon, ya kalleta akidime yace miya faru ?? Tana kuka tace yhu rape me… “Wat ya fada arazane, ya mike zaune, ganin ba kaya jikin sa ya kara tabbar da yuyuwan hakan, da sauri yadau towel ya daura, araunane ya ruko hannuta yace zee am so sorry nikaina bansan inda kaina yake, infact I cnt recall anytn, plz kidaina kuka hop ban ji miki ciwo ba ??? ta shagwaba fuska, am weak kuma nakasa tashi, da sauri ya dauke ta yakai ta toilet ya taimaka mata tay wanka, shima yay yafito, sukai sallah, yana kara bata hakuri tana wani yatsine, agurguje ya shirya dan akwai masu jiransa a office… Hop dai my dautæ is okay ?? ” madam kofo dake waya da umma tay dariya tace tana nan fyn, kinsan she is pretty kowa yana sonta, ba wani trouble, “umma tace yauwa aikin ki nakyau, shiyasa bana wasa da payment dinki duk month, tnx a lot….” madam tace haba hajiya aini ce da godia, “okay toh my regarz to her plz, sukai sallama ta kashe…..” Da sauri ya fito ya iske ta kan dining tana breakfast, yace umma ina kwana ? “Ta amsa adakile tace dan xabagin rashin kunya sai yanxu zaku tashi daga bacci, abba ya jiraka harya gaji ya wuce ” yace sorry ma, ” tace ina fatan baka manta da maganata ta jiya ba ?? yay shiru yana tunanin wace magana kuma, shikam ya kasa tuna komai daya faru daga daren jiya zuwa lokacin daya farka daga sleep…..”yace umma ban manta ba, sai na dawo, ya fice dasauri…. Tana ganin ya fice ta duro daga gado tana murna, koma komai tasan he is sure sunyi s*x, next plan shine ta zubar da cikin, dan ba karamin wahalar ta yake ba…..uhmm *cute Xarah* [09/10 9:23 pm] cute Xarah : *KURSUM* By ~ xarah bukær *Two Months later* Ke Hafsatu!!! hafsatu!!! baba shehu ke kiran sunanta a afusace, ni zaki ma cin mutunci agidana, harki kawo katti hudu su daure ni kaman barawo….”gimbiya ta kece da dariya tace baka da banbanci da barawo, ina takardun gidan da sauran dukiyoyin daka tara ?? “ya kalleta a wulakance, saidai ki mutu dan kuwa bazan baki ba…..” tay shewa saidai kai ka mutu, saboda son abun duniya shiyasa Sam baka damu da tafiyar yayarka ba, toh kasani nice nan na boyeta, babu wanda yasan inda take….”atsorace yace ina kika kaita, wana dalili yasa kika boyeta ?? “Daga ni harkai boyeta yay mana amfanin, da yanxu kursum CE amatsayin da kake, mu kuma muna prison….” yace bangane ba, miya shafi kursum da hajiya….”ta kara karcewa da dariya, to kasani diyar da hajiya ta haifa bata mutu ba, itace dai Kursum din da kake burin kashewa, tun randa nagano gaskia yasa na batar da hajiya, dan nima bana fatan tasan tana da uwa aduniya…. “Akidime yace tabbas kursum jinin muce, nima na dade ina tunanin haka, amma son abun duniya yasa na kawar da tuna nin, ki taimaka ki gayamin inda hajiya take, kuma dole Kursum tasan ni kanin mahaifiyar tace.. ” mugun kallo gimbiya ta wurga mai tace idan har kanason information ka damka min duka dukiyar kursum…..yace bazan bada ba, “tace okay xan baka tym zuwa gobe kayi shawara, ta mike tare da rufe mai baki da saletif, ” yana ihu tare da kokarin kunce kanshi daga iron kujerar da aka daure shi….”ta kece da dariya sannan tafice tama dakin mukulli “hinde dake tsaye bakin kofa tace ya ake ciki ?? ” tace har yanxu yaki bada hadin kai, amma xanyi kokari na kwaci rabona in kashe shi kawai, yauwa ina poison danace ki kawo min ?? “hinde ta bude jaka ta ciro,tace gashi amma ba ruwana wooo, ” karki damu neat work xanyi, yadda baza ai suspecting ba, kedai ki tafi gida, gobe xanxo in sameki…..hinde tace toh sai kin xo, ta fice daga gidan da sauri “na baki izinin ki dauko Kursum, toh yaushe xaki gayama yazid matar sace, ” umma ta nisa xatai magana tagan shi tsaye bakin kofan palon, da alama kuma yaji su, ya karaso ciki dasauri, ya kalli umma yace matar waye ?? caraf abba yace matar kace, kuma gobe xata dawo gidan nan da xama,”arazane yace umma baki kyauta min ba, all diz while matata ce prison bansani ba…. “akufule ta kalle shi, ni kake cewa ban kyauta ba, wato kama manta lokacin daka ce she is dead to yhu…yace eh still dai I have d ryt to knw tunda mata tace, ” takaici ya hanata cewa uffan tay shiru….”xai kara magana sukaji an turo kofa, meerah ce rike da zee, “ganin xata fadi yaje ya rukota, watx wrong?? ” meera tace kusan kwana biu bata jin dadi shine naraka asibiti akayi test, she is 2month pregnant….”wat ya fada afirgice, baiyi xpecting ciki ba cox yasan sau daya sukai s*x, ya kalli zee ina result din ?? “ta bude Jakarta xata ciro ta fadi wanwas sumammiya, ” umma da abba suka mike atsorace, “ya yazid yace karku damu, I tink stress ne, ya sunku ceta zuwa daki ” meerah dake tsaye ta kwashe da dariya, tace kunji kunya wlh, bakwa sonta ashe danku na sonta tunda gashi har ciki ya dirka mata, “umma ta watsa mata harara, marar kunyar banxa, ki ficemin daga gida….” ba sai kun Kore niba, excuse me ta fice tare da murmusa wa…..”abba yace Allah ya sauwake, nikam nayi dana sanin hada auran nan, “umma tace sai hakuri tunda an samu tabo, aranta tana mamakin ace cikin wata biu ne, kusan wata uku da suka wuce take ganin signs din ciki tattare da zee….uhmm sudai suka sani shiga toilet yay ya dibo ruwa ya yayyafa mata, firgigit ta farfado tare da rike shi gam tana kuka, “ya tallafo ta jikin sa yana lallashin ta, tace yaya 4 d sake of our baby plz don’t leave me again, u knw I luv yhu alot n I cnt live witawt yhu….”shsss ya daura finger dinsa kan lips dinta yace calm down 4 d sake of our baby, banaso ki tada hankali, i’ll 4eva b wit yhu, ” tay murmushi tare da kara shigewa jikin shi, dama da gangan tayi sumar karya….”shiru yay yana tunanin Kursum, gaba daya yakasa sukuni, fatan shi bai wuce ya ganta gobe ba Washe gari Tun safe umma ta gama shirin ta tsaf, ta dau car key ta fito, yana tsaye rike da hanifa bakin mota, ganin ta fito ya karasa wajanta da fara’arsa yace umma bari muje da mota ta, ta balla mai harara, ina ruwanka da inda xani, “haba umma gurin dauta xan rakaki, ” tace banso kaje ka kula mai ciki….”bacci take yanxu.. “tace bazaka bini ba, idan kuma ka biyoni ban yafe ba…ta raba ta gefe ta shiga mota taja…” turus yay yabi motar da kallo harta fice Prison Tsaye suke suna bakwana, lady tay hugging dinta tace pretty kar dai ki manta dani, nan da 5years I’ll b release, I hop zaki taimake ni kaman yadda namiki, “Kursum dake sharar kwalla tace lady na dauke ki tamkar family da banda shi, kin kula dani tamkar little sis dinki, nayi alkawari kasan cewa tare dake har karshen rayuwata…..suka dan koka daga bisani police woman (kofo) ta kirata tabata kayanta ta canxa suka fito ta iske umma zaune harta amso release papers tana jiran ta, ” da gudu ta karasa ta rungumeta, tace yau gani ga ummatah umma tay daria tace lailai Kursum kin canxa ba kadan ba, dakyar nagane ki… madam dake tsaye tace nagama aikina, nizan koma ciki, “umma tace ai kinyi kokari mungode sosai, ta masu bye ta koma ciki ” ita da Kursum suka shiga mota, tace muje gida ki cire kayan nan, kiyi wanka ki huta….dumm gaban kursum ya buga, sam bata da niyyan koma wa gidan umma dan ta tabbata zee na gidan,”dakyar tace umma kimin hakuri bazan iya zuwa can ba, banason wani tashin hankali plz ki kaini gidan inna sadiya, hankali xaifi kwanciya….”jikin sanyaye umma tace nasan u need some space, karki damu xan kaiki gidan inna, “tace nagode….” shiru umma tay batace komai ba “tace umma ya labarin hajiya ance min tay tafia, bata dawo bane ??? uhmm hajiya fa labarin ta, nikaina kusan wata uku banganta ba, ko gidan kaje baa bari ashiga cox gimbiya ta bada order…..” akidime tace sumtin is fishy, duk abunda aka hada da gimbiya ba gaskia ciki, Allah yasa dai lapia, “umma tace dnt worry na tabbata she ix okay tunda shehu na gidan….” toh kawai tace amma jikinta na bata sumtn is not ryt. “Suna isowa gidan ta shiga makota ta amso mukulli, “karamin gidane mai dauke da daki daya hade da toilet da falo, komai tsatsaf, suka zaune, “Umma tace barin je gida in kwaso miki kayanki, ta fiddo yan dubu dubu ta bata tace ki rike 4 incase har naje nadawo….tace toh umma ma regardz to hanifa, “daria tayi tace dawa kuma ?? ” tai murmushi tace da abba …..”tayi dariya ta fice Qwas qwas tazo tasa key ta bude kofan afusace, yana nan daure tun jiya agalabaice, ruwa masu sanyi gaske ta watsa mai tare da cizge salitif din bakinsa “afirgice ya bude idanu, tace shehu ina kudin suke ?? yay banza da ita….tay murmushi mugunta ta ijiye poison din kusa dashi,ta fiddo syringe ta xuke poison din ciki tace idan na tsira ma mutuwa xakayi, so am asking yhu 4 d last tym ina kudin suke ??? ” duk ya tsure yace inada 3.9 trillion under bed oda papers na company da gidan basa hannu na suna wajan Kursum…. “da sauri ta leka ta cire katon briefcase dake wajan, ta bude taga makudan kudi, tay shewa tace woww am rich, ” yace kin samu kudin, ina kika kai hajiya ?? ta wurga mai harara, hajiya ta dade da mutuwa kaima yanxu xaka mutu, “yace haba gimbiya kar muyi haka dake, u are my wife bai kamata kimin haka ba, ” hhh aure na dakai is over, ta dau syringe din ta soka mai awuya…..”wani irin kara ya saki agigice ga jini ta baki, hanci da kunne na tsiya ya, sai uban tari yake….”ta kyalkyale da daria sannan tadau briefcase din ta fice da sauri… Tana nan zaune inda umma ta barta, tay shiru, gabadaya hankalinta ya koma kan hajiya, wani irin bugun gaba take ji….kaman an tsigareta ta mike tsaya da sauri, yau dole taje gidan koda xaa hanata shiga, Jikin ta yabata sumtn is wrong, ta fita tasamu taxi yakaita gidan…. “Gidan bude ko mai gadi babu, ta turo kofan palon ta shiga, ta karewa palon kallon babu komai ciki, duk kayan alatun an kwashe, ko tv babu…..ta haura sama, direct dakin hajiya ta wuce, ta murda, bude yake, ta shiga babu kowa ciki, ta tsaya dube dube, ta hango wani karamin kit, ta dauko, tana budewa picx suka zubo, taduba taga picx dinta ne tana jaririya, ta kwashe tana mamaki, aranta tace mayb gimbiya ta kawo su nan….ta fito ta shiga dakinta, komai hargitse ta ganshi, tace kome ake naima anan kuma ohooo, tasan dai kayanta na gidan umma.. ” ta fito xata tafi, tace bari dai na leka dakin baba shehu, ta tura kofan ahankali ta shiga…. “ganin shi cikin mugun yanayi yasata saki kara afirgice *cute Xarah* [11/10 9:01 pm] Cute xarah : *KURSUM* By ~ xarah bukær Aguje ta karasa cikin dakin, ta tallafo shi tare da kokarin sunce shi, ga jini ta ko ina na dalala, “dakyar yace kursum ki yafemin mutuwa xanyi, gimbiya ta kashe ni ” fashewa tay da kuka tare da cewa baba ba xaka mutu ba, kome kayi na yafe….”numfashi sama sama murya na rawa yace ki nemo hajiya itace mamannn……bai iya karasa magana nan ba ya fadi kasa wanwas ba rai, “razanan nan ihu ta saki tare da mi kewa tsaye atsorace, shikenan baba ya mutu take furtawa agigice, ta hango waya kan gado ta dauka da sauri tay dialling no din Dr.Malik…buga daya ya dauka tamai bayanin komai, yace nan da 2mins xai turo ambulance, “tace toh, zama tayi tana zubda hawaye… ” suna zuwa asibiti aka wuce dashi emergency, “ta fiddo wayan tasa no din tay dialing, ” tana daki tana hada kaya taji wayarta na ringing, ta dauka jin murya Kursum araunane yasa ta tsorata, tace miya faru ? “hankali tashe ta tsara mata komai, umma tace calm down ganin nan zuwa asibitin Suna zaune a dinning yana feeding dinta, sai yastine take tana xuba shagwaba, umma ta fito tace ku tashi muje asibiti shehu ba lapia, “tsaki zee tayi, nidai wlh ana bakin cikin kebewa ta da mijina, dan baba baida lapia dole sai mun kwashi jiki munje….tsawa yazid ya daka mata tay shiru ba shiri….umma tace kyaleta ai ubanta ne ba nawa ba, tayi fuu tay waje….” ya kira mai aiki ta kula da hanifa yanxu xasu je su dawo, “koda suka fito umma taja mota ta wuce, Allah yasa keys dinsa na tare dashi, suka shiga mota yaja su.. zaune take tayi tagumi, ” tunanin Kalaman baba shehu take, maman wace hajiya ? ta tambayi kanta…dole ta binciko duk inda take, “ganin umma na tahowa yasa ta karasa wajanta da sauri, umma tace ya ake ciki ?? Mi doctor yace ?? xata kara magana suka ga Dr malik yafito daga dakin, ” hankali tashe kursum tace Dr. Allah sa bai mutu ba, ya sauke numfashi yace anci saan kawo shi dawuri, da poison din daya sha ya kashe shi….”akidime umma tace poison kuma, hw cms ?? Hop dai he is okay ?? “Dr yace he is fyn, saidai poison din yay affecting dinshi ba kadan ba, yasamu temporary paralysis daga bangaran jikin sa na dama….innalillahi wa inna’ilaihi raji’un kursum ta furta, yanxu Dr ba wani treatment da xaku iya yi ?? yace irin wanna ana treatment sai dai ba farat daya xai warke ba amma with tym xai warke tunda temporal ne, ” okay toh muna iya ganin shi yanxu ??? “Yace a’a sai nan da 4hrs tukun….toh sukace tare da samun GU da xama.. Kursum tace umma kinsan kuwa poison gimbiya taba shi, ” kai haba dai…. “wlh kuwa shi baban ke gayamin, kuma yace en naimi hajiya maman watace, ni bangane ba gaskia…” umma tace Allah kadan yasan inda hajiya taje, ga shi ko samira ba labarin ta, “ohh da samira sukai tafiyan ?? tace eh nima shehu ke gayamin kwana ki ” Kursum tace lailai ko akwai wata kullalliya, aiko samira ta taba ban number mamansu kuma na rike, umma tace yauwa buga muji ko suna da labarin samirar, “tana bugawa aka dauka, suka gaisa lapia lau, tace mama dan Allah samira na nan ?? mama tace e tana nan, wake magana ?? tace kursum ce…”yar albarka zaki CE ai, samira na bani labarin ki sosai… Tace inaso zuwa wajanku saidai na manta sunan unguwar taku ?? “mama tace aiko bata da wuyan gane wa, da kin xo tarauni wajan yan burodi kice anuna miki gidan mama mai masa shine gidan namu…” kursum tace nagode sosai mama ganin nan zuwa….sukai sallama ta kashe…”umma tace nasan layin tashi muje…”suna tashi ya yazid da zee suka iso, chak kursum ta tsaya kallon shi, ba karamin kyau da kwarjini yay mata ba, shima ya bita da wani irin azababban kallon so, nan take na sakar masu wakan “Teri meri kahani (Gabbar is back)” tofah :oops::oops: love in d sky “Umma kam dariya ma suka bata, zee kaman ta fashe dan haushi da takaici, tama lura sun manta inda suke, afusace ta ciro 6 inches hill dinta ta wurga mata, kiris ya rage bai bugi fuskan taba, “afusace ya yazid ya kalleta baki da hankali ne, da sauri ya karasa wajan kursum ya rikota yana mata sorry, hop baki ji ciwo ba, ” tay banxa dashi tare da ture shi, umma dake gefe saida ranta ya sosu, “zee tace shegia, yar titi karuwa tun bai nemeki ba harkin kawo kanki gareshi, umma tace koma dai miye matar sace, kuma tafiki sau dubu awajane na,” tay shewa tare da rike kugu, ai dole tafini tunda kina bakin cikin ciki da danki ya dirka minn….tas din kakkaywan mari taji ya yazid ya bata a kunci, yace kinci darajan cikin da kike dashi dayau na sake ki, wawayi marar hankali, ubanki baida lapia baki damuba sai haukan banza kike mana anan “ta fashe da kuka ni ka Mara ko, ai ubana ne baida lapia ba ubanka ba, wlh ban yafe ba, ta kalli kursum ke kuma mu xuba, shegia mayya…ta warce car keys dinsa ta fita waje……” umma tace yau naga ikon Allah, ta kalli kursum da jikinta yay sanyi, ita tausayin zee take ga baba shehu ba lapia sam bata damu ba, umma tace muje kar dare yay mana….. suna tafe yaja hannuta ta baya, ta balla mai harara, fuska tamke tace miye haka ?? yace naga kinyi banza dani, ko muna fada ne ?? aranta tace lailai namiji dan rainin wayo ne, afili tace bansani ba….”yace toh kiyi dariya banaso kina bonie face, “ta kara gimtse fuska, xai kara magana umma ta juyo tace ga keys dina ka kaimu, naga alama marar kunya nan ta wuce da motarka, ” ya amsa tare da Sosa keya…suka shiga mota yaja su har gidan samira…. “Umma da kursum suka shiga da sallaman su, ” samira dake wanki tazo da sauri ta gaida su sannan ta dauko masu tabarma suka zauna, mama ma ta fito suka gaisa…..”kursum tace samira keda akace mana kunyi tapia tare da hajiya, ina kika bar hajiya ?? “samira ta nisa tace wlh karya akemin babu inda naje da hajiya, ” umma tace mun shiga Tara, ina hajiya take ?? ke bakisan inda take ba ??? samira ta sauke ajiyan zuciya tace tabbas nasan inda take…”baki hade sukace tana ina ???? samira ta gyara xama tafara magana…… *cute xarah* [11/10 10:31 PM] cute xarah : *KURSUM* By ~ xarah bukær *Flashback* Aranar da Umma tazo wajen hajiya suka Dade suna hira, bayan ta tafi misalin karfe sha biyun dare lokacin kowa ya kwanta, naji motsi ta bayan dakina, na tashi nafito waje ta baya, naga maigadi na kokarin kashe wani abu awajan, nace lapia me kakeyi anan, yace min ai gimbiya ce tace akwai macizai gurin inxo in kashe su, “nace toh Allah shi kyauta ita dai matan nan kini bibinta yay yawa….na fito xan koma cikin gida na hango haske torch light daga bakin gate, da sauri na karasa wajan, naga gimbiya da antee hinde reke da hajiya suna kokarin turata cikin boot, atsorace nace gimbiya ina xaku kaita ??? ta buga uban tsaki, yarinyan nan ta batamin plans, hinde tace shigo da ita kawai mu wuce, ” haka gimbiya ta turani cikin motan, taja muka je wani asibitin mahaukata, suka kai hajiya wani daki sannan hinde ta sheidawa likitocin ai yayar tace, tasamu matsala kwakwalwa ne, ba shiri suka amsheta dayake hinde nurse CE a asibitin….”daga nan muka fito, muna zuwa babban doguwar titi, gimbiya ta fidda ni daga motan, ta ciro bindiga ta nuna ni dashi tace karna kuskura na koma gidan, duk randa ta ganni kashe ni xatai….”haka suka barni atitin nan ni daya, kusan awanni biu nayi tsaye ba motar data welka daga bisani wani dan albarka akan mashi ya taimake ni ya kawo ni gida…tun ranar ko fita ban karayiba gudun karta ganni ta kashe ni…. *Back 2 story* Samira ta karasa labari tana sharbar hawaye, “umma tace zaki gane asibitin ?? kwarai kuwa xan gane saidai tsorona daya kar gimbiya ta kashe ni, ” Kursum tace karki damu yanxu haka police naiman ta suke akan kashe Baba shehu datai niyyan yi, “samira tace kaico matan nan Sam bata da imani, muje nakai Ku asibitin, suka mike tare dayiwa mama sallama suka fice. Zaune yake cikin mota ganin sun fito yasa ya fito da sauri ya bude mata kofar gaba, ” kaman ta shareshi saidai ta daure ta shiga tare da hura hanci, yay murmushi ya koma mazaunin sa, umma da samira abaya…. Suna isa direct office din babban likita suka wuce, “hinde dake tahowa ta hangosu, ba shiri ta labe, duk ta kideme, shikenan asirin ta ya tonu….” suka ma doctor bayanin komai yace tabbas sunyi gwaje gwaje basuka alamun hauka tattare da patient dinba, mun dai lura she is depressed ko yaushe cikin kuka tare da kiran wata kursum, “umma da kursum suka kalli juna, ” yazid yace tana ina yanxu ??? Dr yace special room muka ajiye ta, bana mahaukata bane…”Kursum tace yakamata Ku dau mataki, tunda nurse hinde kidnapping dinta tay ta kawota nan…. yace ba komai, daga yau mun sallame ta daga aiki, Ku kuma idan kunaso kwayi pressing charges against her, muje in kaiku wajanta….suka mike har dakin da hajiya take ya kaisu….tana kwance duk ta rame, harda tsufan dole, jin motsin mutane yasa ta mikewa zaune, ganin su yasa ta kara fashewa da kuka, “da sauri kursum ta karaso wajanta tace hajiya ki daina kuka munxo daukan kine, ” araunane tace kursum ki yafeni nice mahaifiyar ki, tunda nayar dake ban samu sukuni ba, ga kuma tsanar dana miki aranshin sani dan Allah ki yafemin, “hankali tashe ta dago ta kalli umma, dagaske ne kodai mafarki nake ??? ” umma tace ba mafarki bane, hajiya itace mahaifiyar ki ta jini, dan Allah kiyi hakuri ki amshe ta, “yazid kam gabadaya sun sashi aduhu, shida yake ganin laifin Kursum na boyemai hanifa, ashe itama boye mata mahaifiya umma tayi, haushi kanshi yaji farat daya, balle inya tuna rashin m dayay mata, sai yanxu yasan some secret are kept for some reasons, “kuka kawai take ya karaso yay hugging dinta tare da lallashinta, yace plz 4give us mun miki laifi …..we are sorry, ahankali ta zame jikinta daga nashi, ta dago idanuwa ta da suka sauya launi tace no matter abunda mama na tamin i’ll 4give her cox she is my mom, amma kai yhu are notin to me, i cnt forgive yhu, infact u are dead to me….. ” dumm gaban umma yafadi excatly abunda yazid yace mata take maimaita mai……samira dake gefe itama kukan take, dan tasan ba karamin rashin mutunci da tsane hajiya tama kursum ba “ta zauna tare da riko hannu hajiya tace mama na yafemiki, burina bai wuce inga uwata ba, yau naganta ai bazan kita ba, suka rungumi juna suna kuka, (ni kaina saida na zubda hawaye )…..” suka fito jiki sanyaye, kursum na makale da hajiya suka shiga baya da samira, umma da yazid agaba….”asibiti suka wuce wajan baba shehu, Dr yabasu daman shiga… kwance yake yana bacci abun tausayi, “hajiya ta bishi da kallo tana kuka, tace shehu duk ni najamaka inda ban yar da kursum ba da gimbiya bata shigo rayuwar mu ba, ” kuka kawai take ba kakauta dakyar umma tajata sukai waje, “kursum dake tsaye tama rasa meke damunta farin ciki ko bakin ciki ?? ” yazid dake gefe ya karaso wajanta, “afusace tace don’t yhu dare touch me, ” yace am sorry nasan I misunderstood yhu, plz don’t go we need each oda, “harara ta wurga mai, excuse me I have my mom so I don’t need u anymore, tay tsaki tare da ficewa daga dakin ” ranshi ya baci matuka, ji yake kaman ya tsokawa kanshi wuka ko xata hakura……(ohh ni xarah dama ance first to do no dey pain second to do eye go red ) Tunda tabar asibiti ta wuce gidan meerah, suna zaune apalo suna shaye shayan da suka saba, “tace galfrnd yau xan zubda cikin nan, yana wahalar dani ba kadan ba, it better in zubda tun kafin asirina ya tuno….” meerah tace it risky amma inada pill da zaki sha ya zube in 2mins….”zee tace bani plz….ta shiga daki ta dauko tace gasu kisha guda biyu kawai, “zee na amsa ta hada pills guda goma ta hadiya nan take, aganinta xaifi aiki sharp sharp….After 2mins taji shiru ba alaman xubar komai, tace meerah anya maganin nan na aiki ?? Tace yana yi mana, mayb ko jininki is Strong, akwai wani method idan kinaso….zee tace wanne, indai xai zubda ciki inaso…” tace very simply da hangar xan cire miki cikin…. “galfrnd dauko hangar din muyi trying, nidai nayi alkawarin bazan koma gida da cikin nan ba, tace okay ta shiga daki ta bude wardrobe ta dauko hangar ta fito….tace oya kwanta kiga dabara, ko tsoro babu zee ta kwanta tare da kwangale kafafu….” meerah ta cusa hangar cikin Hq…”saida xee tayi kara dan azaba…..ta murda sannan ta fiddo shi, jini yafara tsiyaya kaman an bula leda, ihu kawai xee take, ganin guda gudan jini na fita sharrr kaman a pampo yasata tsorata, meerah tace don’t worry xai tsaya….. after 20min abu yayi worst duka palon ya baci da jini, xee kam tun tana ganin haske tafara ganin dubu, mikewa tay zata tashi tsaye tafadi wanwas akasa ba rai, “atsorace meerah ta karaso gabanta tana bubbugata, galfrnd tashi mana, watx wrong ?? taji shuru, dukta kidime, da sauri tadau waya ta kira olamide…..cikin minti 10 ya iso , ganin zee kwance cikin jini yasa shi tsorata, ya tabata babu rai, ya kalli meerah, wat did yhu do ??? tace nothing I just help her to abort d baby…..” wat yace arazane, yhu killed my baby…..tace ba laifina bane…afusace yace am calling d police….. *Xarah bukær* *Dedicated to Badia* *Highlight* Next page on kursum *Final* Rike take da Ak47 tace ni zakiyi betraying ??? “atsorace tace a’a kiyi hakuri wlh ba haka bane…..” Ko sauraranta batai ba tay shooting dinta har sau biu:oops: Ana shigowa da ita sukai 4eyes, tayi murmushi mugunta tace we meet again, it pay back time Indai kina sona kuma Nina haife ki yakamata kiyi hakuri kiyi accepting dinshi tunda ya gane kuskuran shi…..tace Mom kyale ni dashi kawai Momy!!! Momy!!!! kinga sis hanifa ko, tace yau bazata je dani office ba, wace ake kira da mum tace haba xee kinsan office ba gurin yara bane, ko hanifa ma dan she is 16 datx y nake barinta taje, toh mom ki kaini gidan antee salma….yara hudu ajera suka shigo tare da daddy suka CE mom muma xamu Hello co- workers…..suka bita da kallo…su dai dariya take basu, yarinyan karama ga kyau da kudi sam bata da girman kai ko kadan…..tana shiga elevator sukai kicibis da …….tace Mom’s PA ina kwana ?? tai dariya tace yanxu naxama PA dinki, ta bata rai banason PA tsofi Tofah yau daurin auran baba shehu:oops::oops: dawa ??? [14/10 11:30 am] cute xarah : *KURSUM* By ~xarah bukær *Final episode* Police na zuwa aka wuce dasu station, “meerah sai kuka take sabanin olamide dayay kicin kicin da fuska (tofah boyz no dey smile), tsarawa Dpo komai yayi sannan yadau wayan zee yay dialing no din baba shehu ” suna zaune asibiti umma tace yakamata su koma gida dare yayi, “kursum ta kalli hajiya tace mama kuje gida xan tsaya da baba, ” a’a kafata kafarki, tare zamu gida enya so gobe ma dawo, “ba masu tace toh, samira kam tuni ta koma gida ” umma tace kira yayan naki mu tafi… “yana nan tsaye inda ta tabar shi, ko kallan shi batai ba tace ana kira, ” jiki sanyaye ya fito, zasu wuce taci fone din baba shehu dake hannuta na ringing, ta duba taga zee ce, ta kalli umma tace zee ke calling, “dauka muji mai xata ce enji umma ” atsorace ta dauka cox a tunanin ta zee CE, daga dayan Dpo ke magana, yay Mata bayanin komai, “agigice tayar da wayan, jiki na rawa ta kallesu tana xubda hawaye, ” da sauri ya yazid ya rikota tare da dauka wayan, yace lapia miya faru? “baki na rawa dakyar tace sis zee ce tarasu…”innalillahi wa inna’ilaihi raji’un umma da hajiya suka furta lokaci daya, akidime yazid yace hw cms ?? waye ya kira ?? tana ina ?? umma tace calm down, bari muji daga bakinta, ta kalli kursum dake kuka tace dauta gayamin mi akace awayan ?? hankali tashe ta larabta masu komai, hajiya ta nisa tace bamu ga ta xama ba, mu wuce police station din… “Suna zuwa direct office din Dpo suka wuce, yana zaune da olamide suna tattauna, suka shigo hankali tashi, Dpo ya basu gurin zama sannan ya kara masu bayani, “hajiya ta kalli ola tace bawan Allah mun gode sosai daka kawo report, ” ya numfasa yace madam ni kaina am a victim cox zee is three month pregnant wit mah child…”harara yazid ya wurga mai, u are not crious matar tawa ce ke dauke da cikin ka ?? “kwarai kuwa bata gayama bane…caraf umma tace I tot as much, na dade ina kokwanto ciki xee, ina kawarta tazo tay mana bayani ” Dpo ya tura sergeant ya dauko ta daga cell, “duk ta fige ta lalace farat daya, aka shigo da ita sanye da handcuffs, ganin su yazid da umma yasa ta fashe da kuka, hajiya tace ba kuka zakiyi ba gaskian xancen mukeson ji, ” ta sauke ajiyan zuciya sannan ta zayyane masu komai dangane da cikin xee da plans dinta na drugging yazid har yake ganin dagaske yay raping dinta, “salati umma tayi tare da rike ha’ba, tace yazid tunda akai auran nan ba abunda ya shiga tsakanin ku ?? ” kasa bata amsa yayi tsananin yadda xuciyar sa ke kuna, ya rasa maisa duk macen daya so saita wahalar dashi, wani irin tsanar zee yaji axuciyar shi, afusace ya bar office din “Kursum dake zaune jigum taji kaman ta bishi, ba karamin tausayi yabata ba, ta tabbata saboda ita yaki kula xee, ” hajiya tace haka Allah ya tsara, dan haka hannuka bazai rube kayar ba, Dpo abamu gawar mu wuce da ita gida ita kuma wanna, ta nuna meerah da tsaya, akaita inda yada CE….”yace ba komai, saidai har yanxu babu labarin hafsatu, mun bincika ko ina bamu ganta ba, tace barta kawai munyafe mata,tunda shi shehu bai mutu ba, indai duniya xata ga sakayya.. “suka fito jiki sanyaye, akasa gawar ta awata mota daban sannan suka shigo tasu yaja, zaune suke shiru ba wanda yace uffan daga bisani umma tace kursum mu je gida kidau kayanki koh? hajiya tace a’a dare yayi sai dai xuwa gobe yazid ya kawo mata, ” okay ba damuwa inji umma Washe gari akai jana’iza aka kaita makwanci ta, “gidan hajiya ciki yake da jama,a yan gaisuwa,”tana zaune a Palo huzaifa da yazida suka shigo, suka gaisa yace hajiya ina kursum?? ga kayan ta……”tace tana daki…ya mike ya haura sama, ” huzaifa yace kakus ya jikin baba shehu?? “Jikin da sauki, bai farfafdo ba, kasan poison din ya cisa ba kadan ba, yace Allah yara sauki…suka dan taba hira, Abba ma yazo yay mata taaxiya tare da murnan ganin diyarta. “ita da salma ke zaune daki suna hira, ya turo kofan ahankali ya shigo, ” mikewa salma tayi ta amshe kayan ta ijiye sannan ta fice,” ya zauna bakin gado tare da kallonta, dakyar tace ina wuni ?? ya amsa ciki ciki, yace ki shirya anjima zamu koma gida, ta kalle shi afusace, nifa ba inda xanyi, auran ma banyi, ka sakeni kowa ya huta, “a araunane yace ni kike gayama haka ?? tay shuru bata ce uffan ba daga bisani ya tashi ya ijiye dairy dinta ya fice, ” aranta tace Allah sarki my yaya, muna nan tare kawai dai I need some space….. “dawo wa palo yay yasamu hajiya yace ta taya shi rokon kursum ta dawo, ” tace gaskia bazata takura ta ba, yay hakuri zuwa nan da kwana biu xatai mata magana, “huzaifa yace bro datx y nace ma baa yanke hunkunci lokacin fushi, gashi yanxu kaxo kana regretting, ” uhmm kawai yace yay shuru. Prison Tafe take agaba yar’sanda na biye da ita abaya, duk ta firgice ganin mugun kallon da prisoners ke mata, suna xuwa cell 009 tace ke tare da kwala mata sandar hannuta, “da sauri meerah ta juyo tana sosa wajan tare da matsar kwalla, ” tace madam miye na duka na ?? harara yar’sanda ta watsa mata sannan ta bude cell ta turata ciki, tsuru tsuru tayi ganin wata tsaye bakin gado ta juya baya, ahankali ta tabota tace excuse me .. “juyowa tay suka hada ido, saida gabanta ya bada dummm, atsorace tace yhu ?? “Murmushin mungunta snake tayi tace yes, at long last we meet again, ina kudi na ?? murya sarke meerah tace uhmm am sorry, I don’t have any cash, ” tace interesting, ta fiddo scissor, tunda nayi loosing finger yau saikin rasa left ear, “meerah tace kiyi hakuri wlh xan naimo inbaki, ” dariya tayi tace it pay back tym, tasa scissor ta cire kunne….wani irin razanan nan ihu tayi, nikaina na tsorata da gudu nabar gun. Yau take shirin barin garin, tun safe take baje a daki tana dirga kudi, “hinde ta shigo amurtuke tace gimbiya kudin fah raba daidai zamuyi tunda adalilinki na rasa aikina, ” hmm wai miye haka ne, tunda naxo gidanki ban huta ba sai damu na kike da inbaki, kije kawai idan nagama xan Kira ki, “toh kawai hinde tace ta fice daga dakin, aranta tace dole tadau mataki akan gimbiya dan tasan ta sarai tana iya waskewa tabar ta ba ko taro,” da sauri ta fita haraban gidan inda gimbiya tay parking motar ta, ta shige karkashi motan ta tsinke brakes din , tay murmushi tace koda gimbiya ta hanata kudin itama bazata rayu taci suba “tana komawa Palo taganta ta fito daki rike da niki nikin kaya, tace oya bani nawa share din, ” dariya gimbiya tay tace lailai ko baki da hankali, kidauka xan raba kudin dake, toh wlh baki isa ba, “hinde tadau waya tace idan baki bani ba xan kira police in shaida masu kina nan…..” kut ni zakiyi betraying ?? “kwarai kuwa ke, bani share dina kawai ” kare mata kallon gimbiya tayi sannan ta xuge jakarta ta ciro Ak47 (bindiga) ta nunata dashi……..atsorace hinde tace ah mai yay zafi haka, kiyi hakuri am just kidding…”gimbiya tace ni xakima bura uba koh?? bata jira amsar taba ta harbe ta aduka kafofinta guda biu, ihu hinde tayi ta fadi kasa timmm……”da sauri gimbiya ta fito tafada motar ta, gudu take shararawa na fitar hankali, tana zuwa highway tahau bridge ganin ansa signal din Men at work yasa tay kokarin danna birki, amma yaki yi da alama ya tsinke, ga mota sai gudu yake, bata ankara ba sai ganin karshen bridge tayi, ihu tayi tare da kokarin bude kofa ta fito amma is 2 late, fadowa kasa motar tayi dammm, mutane dake tafe kasan bridge din suka taso da gudu ganin ikon Allah, mota ta fado daga saman kadar da baa gama ba,ga Kuma boot yabude kudi nata xuba, “suna zuwa akaga mace CE ba rai kanta ya fashe, jinin na xuba, antaru sai kallo ake masu dibar kudi nayi suna waske wa, ” aka kira yan sanda……….(wayyo gimbiya Rip ) “Su hajiya na zaune aka kira aka shaida masu labarin accident din gimbiya da saura kudi daya rage, “hajiya tace Allah yaji kanta, kudin sun yafe abawa almajirai… *weeks later* Baba shehu ya fara samun sauki, yana kan wheelchair, Dr ya sallamo shi yana gida, ba karamin kuka yaiba na rashin zee dan yasan shine silar rugujewar tarbiyar ta. ” hinde tayi nadama ba kadan ba, “ga rashi kudi da kafafu, wani yaro tasamu yake kaita bara titi Hajiya da kursum na tare ko yaushe, ko office bata zuwa, har bauchi taje ta dauko inna sadiya ta kawota gidan dan tayata kula da hajiya, suna zaune adaki hajiya tace kursum yakamata ki koma gidan mijinki shine mutunciki, kofan kaunar da umma ke miki ai yakamata ki hakura tunda ya gane kuransa, ” tace mama kyale ni dashi kawai, “hajiya ta nisa, indai nina haifeki dole ki koma ko bakyaso, ” dariya kursum tay tace haba inaso mana kuma na yadda xan koma amma fah sai anyimin buki “ko kefah inji umma duk abunda kikeso xaai ” buki akai nagani na fada, su salma sune manyan kawa aka kaita gidan mijinta dake governor road, “gida ne mai kyau nagani na fada, umma sai murna take, hajiya ma an dage anyi abun arziki , ” hajiya ta roki inna ta auri baba shehu tunda samira ta dawo aiki , dan irin jinyar sa sai matace kadai xata iya kula dashi, “da murnan ta ta amsa, dama kusan shekara 10 da rasuwar mijinta bata sake aure ba, ” banyan kwana biu aka daura auran su “ya yazid sai murna yake, gashi ga kursum da hanifan sa, zaman so da kauna tare da mutunta juna suke, sukan je gida su kaida umma da abba harma su biya wajan hajiya… *15years later* Yarinya ce yar 16years kakkaywan gaske, cikin takunta mai daukar hankali ta shigo t.B oil company, ta kalli employees din dake zaune open space tace hello co- workers ?? suka bita da kallo suna murmushi, burgesu kawai hanifa take, yarinya karama ga kyau da kudi sam bata dau girman kai ba…..”tana shiga elevator sukai kicibis da lady D, tace mom’s PA ina kwana .. lady tay dariya tace yanxu na xama PA dinki, infact harda bodyguard…. “ta bata rai tare da buga kafa tace banason tsofaffi as PA saidai in goyani xakina yi ?? ” oya toh matso kinsa ke yar gatan momy CE dole in goyaki, “elevator na bude wa ta ruga da gudu tayi office dinta, lady tay dariya aranta tace lyk mom lyk dauta… Momy!! Momy!!! Kinga sis hanifa ko, wai bazata je office dani ba, ” kursum dake danna laptop ta dago tare da zare glass din idonta, ta kalli yarinyar da bata wuce 14yrs ba ta rikota tace haba zee kinsan office ba gurin yara bane, koh hanifa ma dan she ix 16 datx y nake barinta taje….”toh Mom kaini gidan antee salma, tace kibari saddiq, iman, ajmal da aryan su dawo daga gidan granny sai muje, Mom we are back inji iman shigowan su kenan tare da ya yazid, da gudu xee taje tayi hugging dinshi, tace daddy kaini office dinka muhau jirgi, yay daria tare daja mata hanci, yace toh kuje Palo ku kalli cartoon later sai muje ko, tace toh suka ruga duka xuwa palo. “Ya janyo ta jikinsa suka fada kan kado, yay mata peck a kunchi yace I cnt liv witawt yhu My little witch, murmushi tay ta kaimai kiss a lips tace I love yhu more dan life itself *Alhamdulilah* Anan na kawo muku karshen littafina, nagode wa Allah daya bani ikon kammala novel dinnan. kusani arayuwa duk abunda ka shuga shi xaka girbe, kun daiga yadda karshe muguye ya kasan ce a littafin, da fatan xaai koyi da fadakar wa danayi, Allah yasa mu cika da imani, Wanda suka rigamu gidan gaskia Allah yaji Kansu da rahma (Amin) *SADAUKARWA* Wannan littafi na sadaukar dashi ga yar’awata, aminiyata mai kaunata Badia I. Alhassan….(Allah yabarmu tare kawas) *GODIYA GA GROUPS* Xarah’s Novels Mu shaa karatu (Kausar) Afshahar Novels Seemby luff Novels Asy khaleel Novels Maman Nu’aym Novel Qurratul ayn Doc 2 Mrs umar Novels Duniyar Marubuta Khaleesat hydar Novels (Fb) Excellent writers Da groups din daban kira ba duk godiya nake *Ban Manta kuba* Fateema khan Naja’atu wali Aisha Dangusau Jiddoo Ummy saddiq Mrs sadeeq (besty) Zee Alee Antee Suzzie Fatee Bello Ummu suhaym Samira Yusuf Zee hot Zainab Riskuwa Xee muktar *Gaisuwa gareku* Kausar luv Ummi hambali Miss hafcy Pherty Xarah bb Qurratul ayn Nuceey luv Nafee anker Anee Autar hajiya Ummi Aisha Billy sarki Lemcy (mamm khady) Asy khaleel Fazyfashion Mrs jawaheer Ummee Adnan Miss xoxo Eshart tsafe Deeyart Yusuf Safah Al’eeman Lil Da gaba daya yan excellent daban ambata ba Sai kun jini a next novel dina *Mace bakin tulu* Taku har kullum *cute xarah* By HAYATU BABA ZUBAIRU (admin Hayat hausa novels Hausa novels and fashion And Cool novel, makeup and cooking) adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *