Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Tuesday, May 23, 2017

MARWA DA MARWAN

adsense here

Marwa da Marwan 1to7 Leave a reply [10/6, 2:58 PM] Hawwadamary : *MARWA DA MARWAN*. 1 *~By Hauwadamary* (NWA) *BISMILLAHIRRAHMANURRAHEEEEM..* Dedicate to *Memxiey_fulla * Zaune nake a bisa d’an dakalin dake qofar gidanmu ina shan iska kasancewar munyi hutun makaranta,hakan ne yasa ban cika zaman cikin gida ba da yamma duk sai inji na takura matuqa,wannan ne yasa tunda makayi hutun makaranta da zarar yamma tayi sai na fito na zauna ina kallon jama’ar dake shige da fice a cikin unguwar tamu mai qarancin mutane. Hakanan naji yau ina sha’awar d’ora ma masoyana masu qaunar littattafaina sabon littafi a yanar gizo,don a gaskiya na d’an kwana biyu ban d’ora ba,hakanne yasa koda yaushe cikin samun saqon ma’abota karatun littafi na nake wanda mafi yawanci qorafinsu a kan rashin d’orawar tawa ne,nakan basu haquri da karatu ne yayi man yawa kuma ga shirye-shiryen zana jarabawa da mukeyi,tou yau dai na yanke shawarar na fara rubutawa yanda kafin na koma makaranta na samu na qarashe shi tunda hutun namu a yanzu saura sati ukku ya qare. Sai dai kash! tunda na zauna nake faman tunani ko zan samu labarin da zan rubuta wanda ba zai d’auki lokaci mai tsawo ba,wata zuciyar ta bani shawarar kawai na qarashe MUTUM MUGUN ICCHE mana,naga gaskiya idan nace zan qarashe ba qaramin aiki zanyi ba saboda yana matuqar buqatar natsuwa sosai don labari ne mai hargitsi da badaqala duk a tare,moreover ba zan iya qarashe shi ba a cikin sati ukkun da suka rage mana,tou yau dai haka na qaraci zamana ina tunanin mafita amma shiru kake ji wai anyi wa mai dami d’aya sata. Wasa-wasa yau gashi na shafe kwana hud’u ina tunanin labarin da zan rubuta mai sauqi amma ban samu ba,kullum idan zan fita nakan fita ne da littafina da biro haka kuma idan zan koma gida nake komawa da su ba tare da na rubuta komai ba. A zaman da nake a waje na lura da wata mata wacce da zarar an kusa magrib take zuwa ta wuce da mota sai chen naga ta dawo d’auke da yara biyu a cikin motar namiji d’aya mace d’aya da kayan makaranta,wannan ne yasa kai tsaye na yanke hukuncin daga makaranta take d’akko su,ina ankare da yanda matarnan ke faman bina da ido duk idan tazo wucewa har tasa na soma tsarguwa. Yau kimanin kwanana bakwai ina zaman tunanin labari kuma har yanzu dai ban samu ba,kawo yanzu harna haqura da rubutawa saboda hutunmu yazo qarshe,na gama yanke hukuncin idan mun sake wani hutun sai na qarashe MUTUM MUGUN ICCHE. “Assalamu Alaiki” nayi anyi man sallama da wata iriyar murya mai taushi da sanyi, Na amsa gami da d’agowa don gane ma idona mamallakiyar wannan murya,ga mamakina wannan matar ce mai wucewa d’auko yara daga makaranta, sai na fara tunanin to me ya fiddota alhalin lokacin fitartata baiyi ba a yanda nake gani tana fita koda yaushe,Anya ko matarnan ba irin masu satar mutane bace,koma dai da mai tazo nafi qarfinta saboda in Allah nasa a raina, na qara kallonta a sace,matar ba wata babba bace don duka ba zata fi shekaru ishirin da shidda zuwa da bakwai ba kuma kallo d’aya zakay mata kasan naira ta zauna.. Muryar matar ce ta katse man tunanina da fad’in”ko dai baki maraba da zuwa na ne,naga ko tayin gurin zama baki man ba”ta qarashe tana kallona d’auke da murmushi a fuskarta. Nima murmshin nayi kana nace”haba dai,waye yaqi baqo,ki zauna ga wuri”na soma goge mata kusa da ni da handky d’in hannu na. Ta zauna gami da bismillah,daga nan gurin ya d’auki shiru na wani d’an lokaci kafin ta nisa tace”nikam baiwar Allah ba don kada kice nayi maki shishshigi ba da na tambayeki dalilinki na zama nan kullum riqe da littafi da biro kina tunani,shin baki tsoron wata lalurar ta same ki *Hawwa Damary* [10/6, 3:05 PM] Memxyy: *MARWA DA MARWAN*. 2 *~Hauwadamary* (NWA) dedicated to *Memxiey_fulla * A raina nace”ay kin riga da kin gama shishshigin”sai dai kuma a 6angare guda tabbas matar nan tana da gaskiya don gaskiya yanda nake cika ma qwaqwalwata tunani ba abunda zai hana wata lalurar ta same ni,na qara kallonta cikin ido kana na sakar mata murmishi a karo na biyu tun zuwanta gurin sannan nace”haka ne,nima wallahi ina so naga na rage tunanin amma bai yuwuwa” “Bai yuwuwa?” Ta buqaci qarin bayani kana kallo na, “Kai matar nan akwai zaqewa” nace cikin raina,nayi kamar bazan fad’a mata ba,sai wata zuciyar tace na fad’a mata kawai maybe ta taimakeni,hakan kau nayi sai na samu kaina da zayyane mata kaf matsalata ta dalilin zamana da littafi da biro, Ga mamakina sai naga ta kwashe da dariya harda qyaqyatawa,hakan ba qaramin qular da ni yayi ba naji dama ban fad’a mata ba yanzu gashi nan ta maishe ni mahaukaciya,eh tou mahaukaciya mana,tunda irin wannan dariya sai kaga abun dariya zaka yi ta ko kuma idan kaga mahaukaci. Saida ta kusa minti d’aya tana dariyarta sannan ta natsu tace”in don wannan ne kada ki samu damuwa,gobe gurin qarfe sha biyu na rana kizo gidana da littafi da bironki ni kuma nayi maki alqawari zan baki labarin da zaki rubuta ma masoya littattafanki wanda zai fad’akar dasu ya tunasantar da su abunda mafi yawanci mutane suka shagala suka manta sannan a 6angare d’aya ya nishad’antar da su,labarin da zan baki labari ne da ya faru a kan qawata ko ince maki aminiya ta,labari ne dake cike da abun al-ajabi,tashin hankali da kuma tsantsar damuwa ga wad’anda abun ya shafa” sai kuma naji tayi shiru, na d’ago don ganin dalilinta nayin shiru sai naga hawaye na zuba daga idanunta, nay saurin cewa”subhanallah! mai yayi zafi haka y’aruwa,idan har labarin da zaki bani ne sanadiyyar zubar hawayenki tou na haqura,wallahi ki bars…tay saurin tsayar da ni ta hanyar d’aga man hannu tace”ni nayi niyyar baki labarin nan don haka kada ki damu,ina jiranki idan Allah ya kaimu goben, ba don kada kice na cika tambaya ba da na tambayeki sunanki” Nayi murmushi nace”ba wani abu ae,sunana Hauwa’u amma anfi kirana da Hauwa Damari” Tace”tou Hauwa Damari sai kinzo” Har ta juya nay saurin cewa”sai dai gashi bansan gidannaki ba” “Ops kinga nima na sha’afa ban maki kwatance ba,kinganshi chen” ta nuna man wani had’ad’d’en gida dake qarshen wanda ba’a dad’e da gama gininshi ba don a tunani na ma ba’a kaiga tarewa ba, Nace”tou sai kin ganni goben” Tay murmushi sannan tace”ki rinqa had’awa da in Allah ya kaimu saboda bamu keda goben ba,kai kana taka ne shima mai goben yana tasa” Nace”hakane,tou ubangiji Allah ya kaimu goben” Tace”Ameen”sannan ta nufi motarta wacce sai a lokacin na lura da ita,nima juyawa nayi na shige gida don ji nayi yau zaman wajenma bazan iya ba, Washegari tunda nayi sallar asuba ban koma gado ba,hakanan kawai naji ina cikin farinciki nasan hakan bai rasa nasaba da labarin da za’a bani,a gurguje na gama taya ummana aiki sannan na wuce nayi wanka,d’akin su qannena na leqa na kira momi da Hafsat nace suy maza suje shagon Abu tela su amso man d’inkina, aiko ba sufi minti biyar da fita ba sai gashi sun dawo man da d’inkin na amsa na wuce na sanya sannan na d’akko gyalen da na tanadar ma atamfar na rataya na fice,dai-dai zan fita parlour naji motsin umma a kitchen nayi sauri na sali6e takalmana na riqe a hannu don kada taji qara ta hanani fita,ina fita na saka na doshi gidan da matar jiya tayi man kwatance. Tafiyar minti hud’u kachal ta sada ni da gidan matar,tsayawa nayi gaban tafkeken gate d’in gidan na qare masa kallo sannan na qwanqwasa,wani figigin buzun mai gadi ne ya leqo yana tambayar wanene, nace masa gurin matar gidan nazo,ko tana ciki? Yace”eh wa za’a she mashi” “Oh ni y’asu,qarfi da yaji ya maida mace namiji” nace masa yace Hauwa Damari, *hawwa damary* [10/6, 3:08 PM] Memxyy: *MARWA DA MARWAN.* 3 *~By Hauwadamary* (NWA) Dedicated to *Memxiey_fulla * Bayan kamar minti biyu da tafiyarsa sai gashi ya dawo yace”yashe ka higa” Nace”tou” na fiddo naira d’ari biyu daga cikin jakkata na miqa masa,yay ta faman zuba godiya,kai gaskiya bacin naga alamar buzu ne da wallahi ba abunda zai hana nace bakano ne. Gaskiya gidan ya matuqar burgeni sai faman kalle-kalle nake kamar wata bakanuwa a birnin zazzau, ban ga abun kallo ba saida na shiga daga cikin parlour da sallamata, Da fara’arta ta taso ta tarbe ni,yauma taci ado kamar kullum saidai na yau har yaso ya zartar da sauran lokutan da nake ganinta, Hannuna ta riqe tana fad’in ae na d’auka ma kin fasa zuwa” nace “ae ba yanda za’ae naqi zuwa tunda har kau ni na furta hakan” na qarashe maganar a dai-dai lokacin da muka zauna saman kujera,ta shiga qwala wa mai aikinta kira,kan kace me an cika gabana da kayan tarbar baqo, Ta kalleni da murmushi a fuskarta da alama taji dad’in zuwannawa sannan tace”tou Hauwa Damari bismillah” Cikin d’an jin nauyi nace”wallahi Alhmdullah saida na cika cikina na fito gida”na qarashe da fara’a Kafin ta kuma magana wayarta dake bisa center table ta soma ruri,ta kai hannu ta d’auka ta soma magana tana kashe murya gami da wani langa6ewa sai ka rantse wanda take wayar dashi yana ganinta ne, hakan da na gani ne yasa na fahimci da mijinta take don haka nima sai na d’auki wayata na soma diba saqonnin mutane ta cikin WhatsApp. Bayan ta gama wayar kuma ta shiga lalubar wata number,bayan an d’auka naji tace”kuluwa don Allah idan kinje d’aukar su miemiey ki had’a dasu daddy da daddare zanzo gidanki na d’aukesu” Banji me aka ce ba naji tayi dariya tace”ke dai baki da dama wallahi,yanzu banda lokacinki ina da abunyi”ta katse wayar, mai aikinta ta kuma kira ta zayyana mata irin abincin da take buqatar ayi,bayan ta gama magana da ita ta juyo gareni tace”kiyi haquri don Allah inata 6ata maki lokaci” Nayi d’an murmushi nace”laaa!wallahi ba komai” Tace”tou bari na soma baki labarin” Nace”don Allah d’an tsaya na shirya” Tace”tou” Na bud’e jakkata na fiddo littafina da biro sannan nace”na shirya” Tayi dariya sannan ta fara kamar haka….. *********** Tsadadden agogon dake d’aure a tsintsiyar hannunsa ya diba,qarfe 7 da rabi na dara harma ta gota da minti d’aya,tsaki yayi tare da maida dibansa ga abokannasa yace”dallah malamai idan zaku tashi Muje ku tashi lokaci na wucewa,idan kuma ba zaku tashi ba ni zan wuce wallahi,dad’in abunma nasan hanya” Umar dake chen gefe guda yana danna waya yay saurin cewa”kunji d’an iskan ba,tou ka tashi ka tafi mana,ay mu ka hutar da mu ma,ko ya kace aboki” ya kalli salim. Dariya salim yayi sannan yace”wallahi kau gaskiyark..”bai qarashe maganar dake bakinsa ba wayarsa da ke gaban aljihun rigarsa ta soma ruri,yace”yawwa ga salman d’in nan yana kira nasan ya qaraso”bai jira cewarsu ba ya kara a kunne, Ta6e baki Marwan yayi ya juya masu baya cike da jin haushinsu don shi da son ransa ne baiqi a ce yanzu yana gaban masoyiyarsa ba,marwansa mai kyau da iya ado,ga tsafta gata da iya tattausan lafazi ba don kada ace ya cika ta ba da sai yace duk fad’in duniyar nan ba macen da ta kai marwansa,haka zai iya bugun qirji a gaban ko waye yace duk mazajen duniya ba Wanda ya kaishi sa’ar mace kamila,mai addi’i na boko da islama,ga girmama na gaba,murmshi yayi gami da lumshe idonsa,yana ji salim nayi wa salman tsiyar ya dad’e yay banza da su.. ********* A 6angaren su Amarya tunda aka watse ya rage daga ita sai qawayenta memxy kuluwa,su suka Kama Mata suka gyara babban gidan nata,sannan suka sake shiri suka zauna zaman jiran angwaye, memzy fad’i take”Allah kuluwa sakin baki zaki mu wanke su don kinga Amaryar tamu ba gajarabul bace” Kuluwa tace”Ashe d’aya muke nima wallhi tun d’azu nake wannan tunanin” “Yawwa shiyasa nake sonki qawas” cewar memxy,suka saka shewa tare da tafawa. Marwa ta hararo su tace”kunsan Allah,duk wacce ta wankan man ango sai na 6alla ta” Suka kalli juna suka kuma kwashewa da dariya kafin kuluwa tace”su ango anji jiki,dad’in abunma muma mun kusa yin auren,sai dai kiyi ma su o’e”ta qarashe tana kallon memxy da gefen ido d’aya. Memxy tayi tsaki tace”jaka kyadai ji dashi” “Kanbu!aiko saikin fad’i man uban da kikace ma jaka” ta qarashe tana qoqarin qarasawa inda memxy take. Cikin sauri memxy ke fad’in”haba Aunty kuluwa,kema dai kinsan bazance maki jaka ba,ni d’in banza”nan fa ake ga tsoro ga jan fad’a. Marwa tay saurin cewa”wallahi ku sauka qasa kuyi wasanku kada ku 6alla man kujera a banza,ku da har yanzu baku girma ba,da kun had’u sai kun saida hali” Memxy ta bud’e baki da niyyar maida mata sukaji qarar shigowar motoci *Hawwa damary* [10/6, 3:10 PM] Memxyy: *MARWA DA MARWAN.* 4 *~By Hauwadamary* (NWA) Dedicated to *Memxiey_fulla * Da hanzarinsu suka tashi suka kuma y’an gyare-gyaren jikinsu,suka feshe gurin da air freshener ya had’e da sanyin AC dandanan parlourn ya bada wani sanyayyen qamshi, Salim ne ya soma kunno kai da sallama sai uban gayyar ne ke biye da shi,salman da umar ne a baya. A ciki-ciki suka amsa sallamar tasu ba tare da sun dibesu ba, salim da bai gani ya qyale ya qare masu kallo sannan yace”yoo ina y’anmatan amaryar ne,ko kuna nufin kuce ku biyu ne kachal?” Memxy ta d’ago ta zabga masa harara dama chen ta lura shi d’an rainin wayau ne,shiko kallonta yay yayi dariya dama abunda yake so yaga tayi kenan,don yarinyar ba qaramin burgeshi take ba,kuma ya lura y’ar bala’i ce ga tsiwa.. Umar dai tunda ya qyalo masoyiyarsa kuluwa ya koma kusa da ita ya zauna,dama shine gwanin nata don yanzu ma baifi sati ukku ya rage suma ayi bikinsu ba,su salman ma zazzaunawa sukay daganan aka shiga hira cike da barkwanci,salman da yafi sauran malumta shine yayi ma ango da amarya y’ar nasiha irin ta abokai daganan ya rufe da addu’a lokacin qarfe tara saura, Marwan da yaga basu da niyyar tafiya yace”malamai yafa kamata ku tafi gida hakanan,kunsan bai dace ace gwauron mutum yana dad’ewa a waje ba” “Allahu Akhbar! Asheikh marwan” cewar salim” sai yanzu kenan kasan da hakan,da kai da kake….” Yayi qwafa”bari dai abar kaza cikin gashinta” Umar yace”ae gara a figeta kowa yaji” “Bar d’an iskan ma kada ya fige ae yasan ba abun figewar ne”inji marwan Salim yace” au haka kace ko?” “Eh,haka nace” Salman dai na daga gefe yana masu dariya don shi dama chen ba ma’aboci son magana bane don ma dai Allah ya had’a shi da irinsu salim. Marwa a ranta tace”oh!Ashe haka yaya marwan yake barkwanci a cikin abokansa,ji yanda yake ta faman annashuwa kamar bashi bane dariya keyi ma wuya,koda yake ai abokai daban haka y’an uwa daban,ko ni idan cikin mutane ne ban fiye ganin fara’arsa ba sai dai idan mun ke6e,amma tunda har na gane haka na d’au alwashin saka sa annashuwa a koda yaushe” kamar daga sama ta tsinkayi muryar abokan nasa suna fad’in zasu tafi sai sun dawo rad’in suna,salim yay saurin cewa”sai dai kin rinqa haquri da wannan mutumin a gurin ci,ba qaramin rumbu bane a sati sai ya gama da buhun shinkafa”ya qarashe maganar yana d’an bubbuga kafad’ar marwan,duka y’an gurin suka sa dariya,marwa ta d’ago suka had’a ido da marwan sa faman mazurai yake shi ala dole ga babba kada taga yana dariya ta d’auka ko da gaske cinne da shi, Ta sadda kanta qasa tana murmushi,ya matso dab da ita ya riqe hannunta ya murza da d’an qarfi yace”wa kike wa dariya?” Ta d’an 6ata fuska kamar zatay kuka tace”kai yaya da zafi fa” Gira ya d’aga tare da kashe ido d’aya yace”I know” Umar yace”kai malam muje ka raka mu sannan ka dawo” Yace”tou kuyi gaba ba sai kun tasa ni ba kamar wani yaronku” Sukay dariya sannan suka miqa ma y’an matan amarya 50k kud’insu na sayen Baki,dama salim yace sai za’a tafi zai basu. *Hawwa Damary* [10/6, 3:14 PM] Memxyy: *MARWA DA MARWAN.* 5 *~By Hauwadamary* (NWA) Dedicated to *Memxiey_fulla * Suna fita umar ya d’auki kuluwansa suka qara gaba,salman ma ya wuce don shima nan cikin barhim d’inne gidan iyayensa yake. Nan memxy ta soma tsurewa ga dare yayi sosai ga unguwar so silent baka jin komai sai kukan karnuka,gashi ko kafin ta kai titi na samu napep aiki ne ba d’an qarami ba,ga tanata kiran number yayanta baya picking,abu ne ya had’e mata goma da ishirin, “Ke shigo muje” a firgice ta juyo dafe da qirji don ba qaramar razana tayi ba,ba kowa bane sai salim”tou shi kuma yaushe yazo,ko dai tunanin da take ne ya hana ta jin qarar motarsa?ba shakka haka d’inne” “Ke ki shigo mu tafi dare nayi” ya qara mata magana,”lallaima mutuminnan wai ke aiko ke saita shiga” duk maganar nan tana yin su ne cikin ranta,ta d’ago ta kallesa cike da tsiwa,taga yay murmushi ta gefe d’aya sai yay mata kama da jaruminnan d’an qasar Philippine(Enrique gil), Fasa yin abunta tayi niyya tayi,tayi d’an siririn tsaki sannan ta juyar da fuskarta, “Lallaima yarinyarnan,” yace gami da figar motarsa ya wuce, Wani qululun baqinciki ne yazo ya tokare Mata a qirji,sai ta soma datasanin qin binsa da tayi, Bayan kamar minti biyar da tafiyarsa a lokacin tsoro ya qara lullu6eta,wata mota ce ta dalle mata ido da fitilar mota,kafin mai motar ya qaraso ta ranta ya qara 6aci da mai motar sai da ya qaraso taga ba wani bane fache salim, dama tasan tatsuniyar gizo bata wuce ta qoqi,tunda taga irin dallare idon, Yana qarasowa yace”ke shigo muje kada ki tsaya girman kai wani yazo ya kashe ki cikin duhunnan” Bata ce komai ba ta shiga qoqarin bud’e baya ta shiga don itama a yanzu bata iya bari ya kuma wucewa, “Heeey!” Yay mata nuni da gaba da bakinsa”i’m not ur driver” Nan ma bata ce komai ba ta rufe bayan ta bud’e gaba ta shiga, Sunyi tafiya mai nisa ya rage sautin kid’an dake tashi yace”ke ina mukayi?” Tayi kamar bata ji shi ba saboda ta tsani ke d’in da yake kiranta da shi, A d’an hasale yace”da ke fa nake kika qyale ni” Itama a qule tace”malam ni fa ba sunana ke ba,idan baka cewa maymuna sai ka bari” Shima yace”nima ba sunana malam ba idan baki cewa salim sai ki bari,ay ba’a dole ko?” Ya qarashe yana kallonta don jin,juyawa tayi ta kalli window,yay dariya sannan yace”toh maymuna inane unguwarku?” Tace”g.r.a ring road near little angels school” Yace”Ashe ma duk kusa muke,mu muna a kangiwa road ta bayan little angels,kullum idan na fito strolling ta gaban gidanku ma nake bi kenan,ina da aboki ta gurin wani abbaty sambo” “Tou fa!dama wannan yaron yasan yaya abbaty” ta fad’a a ranta,haka yayta janta da hira har suka iso, ta nuna masa gidan,yay dariya yace”Ashe ke sister abbaty ce,no wonder kike da tsiwa” Tay murmushi tace”thanks” ta juya ta nufi gida shima murmushin yayi daga bisani ya tada motarsa ya nufi gida…. ********* ASALIN MARWA DA MARWAN Mahaifin Marwan Alhj Mansur Umar Sambo da mahaifiyar Marwa Hjy Mariya Umar Sambo, babansu d’aya haka ma mamansu d’aya su kad’ai iyayensu suka haifa,asalinsi y’an jahar katsina ne cikin 6atagarawa, Sun taso cikin had’in kai da qaunar junansu duk da kau shi mansur ya girmi Mariya da shakaru bakwai,yanda yake sakar mata fuska baisa ta rainashi ba sai ma wata shaquwa ta y’an uwantaka da ta shiga tsakanimsu.. *hawwa damary* [10/6, 3:16 PM] Memxyy: *MARWA DA MARWAN.* 6 *~By Hauwadamary* (NWA) Dedicated to *Memxiey_fulla * Bayan an aurar da Mariya shima ya had’a kayansa ya nufi America qaro karatu a cewarsa gidan tunda ba Mariya ba zai dad’i ba,kafin dawowarsa ne Allah yay ma iyayensu rasuwa a hanyarsu zuwa Cairo ganin likita kamar yanda suka saba duk bayan wata shidda sukanje medical checkup. Wani babban d’an kasuwa Hjy Mariya ta aura duk garin ba Wanda bai sanshi ba da zarar kace Alhj Salmabu mai daloli ba,wasu sukan kirasa da mai daloli kawai,saida suka shafe shekara sha d’aya Allah bai basu haihuwa ba,duk asibitin da suka je sai ace matsalar daga mai daloli take,wannan yasa yaba hjy Mariya shawarar taje ta auri wani kada ya d’auki alhakinta tace ita zama dashi daram mutu ka raba, a cikin lokacin har mansur ya qare karatunsa na shekara hud’u ya dawo gida ya samu mata nan maqobtansu mai suna Asma’u ya aura,da shekara ta zagayo ta haifo d’anta namiji mai kama da babansa sai dai duhun mamansa ya biyo,da ran suna ta zagayo aka saka masa MARWAN. Marwan nada shekara tara a duniya Allah Ya ba Hjy Mariya ciki anyi murna sosae,shekara na zagayowa ta haifi d’iyarta mai kama da ita komai da komai,tunda ta isa duniya Marwan yake zuwa d’aukarta,kullum sai dare drivrnsa ke d’auko sa wani lokacinma a chen yake kwana,ana gobe suna ya dami ummansa(Hjy Mariya)da yake sunan da yake kiranta dashi kenan,shi lallai sai dai a sanya ma baby MARWA, umman tasa da yake y’ar taya 6era 6ari ce,Mai daloli na shigowa tace ga sunan da take so,yace,shikau yay mata Alqawarin sunan zai sanya mata. Washegari suna kau yarinya taci suna MARWA, anyi shagulgula iri-iri sai ka rantse bikin wata y’ar gwamnan akeyi sai an fad’a maka suna ne zaka cika da mamaki, Kullum da zarar an d’auko su Marwan daga schl zaice ma sani driver ya fara ajje shi gurin ummansa sai ya wuce dasu firdau gida,(mai karatu fitdausi wacce ake kira firdau qanwa ce ga marwan ya girmeta da shekara ukku sai ita kuma ta girmi y’an tagwayen Hajiyarsu da shekaru biyu,hassana da usaina) Lokacin da Marwa ta shiga shekara ta shidda a duniya shi kuma Marwan ya kammala karatunsa na secondary yana da shekara sha bakwai,Alhjinsa ya nema masa gurbin karatu a America,ranar da zai tafi shi kuka Marwa kuka duk da qarancin shekarunta a lokacin, Shekaru sukayta tafiya,sai da Marwan ya shafe shekaru goma sha biyu bai dawo gida ba,don harya fara aiki a chen,sai dai kullum suna waya da kowa kuma yana jin duk halin da suke ciki,Marwansa kau musamman ya aika mata da waya don su rinqa gaisawa,aiko tun daga sannan ko abinci zata ci sai ta kira shi shima haka, wasa- wasa suka saba da juna,akai-akai sukan yi family picture’s su tura masa shima haka,shi da Marwa ko kullum cikin tura pics suke duk inda yaje zai yi ya tura mata itama haka,sai shaquwa ya juye ya koma soyayya tsantsa,duk wani dake tare dasu ya san sun shaqu sosae,daga 6angaren Aminansa na America har 6angaren qawayenta itama. A cikin shekara ta sha biyunne Alhjnsa ya matsa sai ya dawo gida,ba yanda ya iya dole ya fara shirin komawa nan da sati ukku dama abokanansa tuni sun koma,sai dai yaci alwashin da zaran ya koma zai sanar da Alhjnsa komai na game da tsakaninsa da Marwa don har kawo yanzu iyayensu basu sani ba, Tunda Marwa taji yayannata zai dawo ta soma murna,kusan ma tafi kowa farin ciki, cardboard paper ta siyo tayi calendar ta liqa saman gadonta da ta tashi daga bacci sai tayi cancelling a haka har ya rage sati d’aya,oasis bakery taje tace ayi mata cake babba a rubuta welcome back bro ko nawa ne zata biya,taje heart to heart ta sayi had’add’un cards masu kyau da tsada sai ta sayi wrapping paper’s da qatuwar gift bag, bayan ta bar nan kai tsaye jifatu ta nufa,jallabiyoyi ta dingi jida dama ita sune kayan sawarta kasancewarta d’aliba a Al- qalam University Katsina tana karantar English Language, Bayan ta gama sayayyar ne taci karo da firdau ta kawo Hassana da Usaina suma sunzo shopping,suna ganinta Hassana tace”tou shanshani sarkin yawo,mun biya maki umma tace kina nan,dama Alhj ne ya bada kud’i yace kowa ya sayi abunda yake so da kuma abunda zai ba yaya Marwan gift” Tay murmushi kawai ta bisu tana so tace masu ta saya kuma tana tsoron suyo mata chaa da zolaya kasancewarsu abokan wasanta da yake y’an mace da y’an namiji suke,basu suka gama sayayyar ba sai yamma.. *hawwa damari* [10/6, 3:19 PM] Memxyy: *MARWA DA MARWAN.* 7 *~By Hauwadamary* (NWA) Dedicate to *Memxiey_fulla * A 6angaren Marwan ma hakance ta faru,tunda ya sami visa yaga ya rage saura sati biyu ya tafi ya soma shirye-shirye da saye-sayen kayan tsaraba,komai ya gani idan har ya burgeshi sai ya d’aukar ma qannensa su hud’u,Firdau,Hassana,Usaina sai Marwansa. Ranar daya rage saura kwana biyu ya koma tunda ya tafi office yay sallama da kowa,turawan kowa jikinsa yay sanyi sunyi matuqar sabawa dashi,dukansu har y’ar dinna sukay Alqawarin had’a masa a gidan ogansu da daddare ana gobe zai tafi,yay murna sosae don karamcin da suka nuna masa, Bayan ya bar office shopping ya tafi,bai dawo ba sai yamma, Washegari ya gama shirinsa ya had’a komai da komai nasa don tunda asuba zai tafi,gurin maqobtansa ya rinqa shiga yana yi masu sallama,kowa jikinsa yay sanyi,lokacin da ya dawo yamma tayi kai tsaye wanka ya fad’a,bayan ya fito ya gabatar da sallar magrib yayta azkhar har aka lokacin lisha yayi ya gabatar da ita ma sannan ya soma shirin zuwa dinner da ogansu ya shirya masa, Tun daga bakin qofar gidan yaga an rubuta”we wl surely gonna mss u blacky”(sunan da suke kiransa) yay murmushi sannan ya shiga,yayi mamakin ganin duka coworkers d’insa duk sun iso,yay murna sosae ya biyu d’aya bayan d’aya yay hugging d’insu,yazo kan ogansu wasu zafafan qawalla suka zubo masa,ogannasu ya dafa kafad’arsa yace”c’mon don’t cry,be a man okay? ” Ya gyad’a masa kai sannan yace”thanks alot” “For what?” “For everything u have done to me,i’m really grateful”ya qarashe maganar yana qaqalo murmushin yaqe Wani Johnny Wanda suka fi shiri dashi shi yazo ya riqe masa hannu ya zaunar bisa table daga nan suka soma cin abinda ke gurin,anayi ana raha kowa na fad’in farkon had’uwarsa da blacky, haka suka watse cike da kewarsa. Qarfe sha d’aya da rabi agogon Nigeria ya buga kuma a dai-dai lokacin jirginsu Marwan yay dirar mikiya a filin jirgin Malam Aminu Kano dake cikin jahar kano, A hankali mutanen dake ciki suka soma sakkowa kowanne d’auke da annuri a fuskarsa,Marwan shine na biyar d’in sakkowa yana gama sakkowa ya hango Alhjinsa da Abbansa Mai daloli sunata faman d’aga masa hannu don ya gansu,da hanzarinsa ya qarasa inda suke ya rungumesu d’aya bayan d’aya,ba qaramin dad’i Alhj Mansur yaji ba ganin d’iyan nasa cikin qoshin lafiya,ya qara zama babban mutum yayi kyau duk da kasamcewarsa baqar fata amma irin baqinsa mai kyau ne,ga y’ar qibar daya yi sai tayi masa kyau sosae,sanye yake da qananun kaya kasancewar inda ya fito ba manyan kaya ne dasu ba, Bayan sun gama gaisawa da kwashe kayansa kai tsaye restaurant d’in cikin airport d’in suka nufa suka cika cikinsu sannan suka gabatar da sallar azahar sai suka doshi hanyar jahar Katsina, a mota sai faman qorafin ba’a zo masa da Ummansa da Hajiyansa ba, Mai daloli yay dariya yace”tou kai in banda abunka ae gurinsu zamu je” Yace”eh nidai Abba duk da haka da anzo man dasu na gansu” Alhj yace”kai dai kana ji da iyayennan naka,ae da mun sani ma su muka bari suka zo d’aukar taka,ko ba haka ba Mai daloli” Abba yay dariya yace”haka ne kam” haka suka cigaba da hirarsu gwanin ban sha’awa. A gida Marwa tun safe ta kira qawayenta tace suzo su taya ta yi ma yaya Marwan abincin tarba, [8/30, 9:13 PM] damary9001: Ba’a d’au lokaci ba Suka iso, Maimuna wacce yawancin mutane ke kira Memxy d’iyar Aminin Mai daloli ce kusan a tare aka haifesu da Marwa,kuma unguwarsu d’aya haka tare sukayi karatu tun daga yarintarsu har kawo yanzu,yayanta d’aya Abbaty Sambo sai Hauwa Muhammad Rimi wacce ake kira Kuluwa itama d’iyar aminin Mai daloli ce itama tsarar su Marwa ce kuma itama tare sukay karatu sai dai ita gidansu suna da yawa, su ukkun duk tare suke sunsan sirrin junansu kaf,don da suna Ulul- Albab yawancin mutane sun d’auka y’an uwa ne saboda ko visiting za’a zo masu a tare ake zuwa masu. Tun kafin kace me gida ya d’auki qamshi,abinci suka had’a kala-kala da zarar Umma ta shigo zasu ce su dai ta barsu su kad’ai zasu yi,ko su riqo hannunta su kaita parlour su zaunar su kunna mata kallo,ita ko sai faman binsu da murmushi take,a ranta Addu’a take Allah Yasa ma MARWA DA MARWAN son junansu har su kaiga aure don a iya tunaninta ba wanda Marwa zata aura ya riqe ta da Amana kamar Marwan haka shima ba wacce take ganin zai aura tayi tattalinsa kamar Marwa,haka tayi ta tunaninta ita kad’ai daga qarshe da taga zaman kad’aicin ya isheta ta kira mijinnata tace tana so taje gidan yayan nata don a tarbi d’an nata da ita, yay dariya sannan yace”wannan d’a dai ana ji dashi,kije ba damuwa ae muma mun kusa charanchi” Tace”tou nagode nawan Allah yabarmu tare” Yace”Amin gimbiyata” Bayan sun gama ta shirya ta leqa gurin yaran tace idan sun gama komai sun shirya su kwaso komai suzo suzo gidan Alhj, suka ce”tou” A chen ma gidan Hajiyan tana zuwa ta tadda Hajiyan zaune parlour ita kad’ai tana kallo,tace”ah!Ina yaran suka tafi ne?” Tace”inafa,suna kitchen suna shirya ma yayan nasu Abinci sunce kada naje su kad’ai zasuy” Umma tay dariya tace”munyi Anko kenan toh ae sai mu tsaya nan muy kallo mu jira isowar d’annamu” Daganan suka cigaba da kallonsu sunayi suna hira jefi-jefi.. Marwa da Marwan 8to11 Leave a reply [10/11, 4:19 PM] Hawwadamary : *MARWA DA MARWAN.* 8 *~By Hauwadamary* (NWA) Dedicate to *Memxiey_fulla * Sosae yayi mamakin ganin yanda aka gyara gidan nasu kamar gidan wani gwamna,ga wasu fulawowi masu kyau wad’anda Suka qara qawata harabar gidan. Tunda motar tasu ta tsaya yaran suka firfito da gudu suna masa oyoyo,binsu kawai yake da murmushi don ba qaramin girma yaga sun qarayi masa ba,duk da daman a hoto yake yawan ganinsu,oh yanzu ko ya Marwansa ta koma? Bayan an shiga parlour an zazzaune suka gaggaisa sai suka shiga hirar yaushe gamo,shiko uban gayyar sai zuba ido yake yaga ta inda Marwa zata fito Amma shiru kake ji ba amo ba labari. Umman tasa ce ta lura da yanayin nasa ta d’auki waya ta kira Marwa tace me take yi ne har yanzu bata qaraso ba,tace tana hanya yanzu zata iso bada dad’ewa ba, Marwan najin haka ya miqe yace zai d’an watsa ruwa,Hajiya tace”au,ni inace sai ka fara cin Abinci sannan” Yace”no Hajiya zanfi jin dad’i idan na fara watsa ruwan,kuma na kira su salim sunce gasu nan qarasowa,nasan idan suka qaraso zaiyi man wuya nayi wankan” Tace”tou ay shikenan”. Kai tsaye d’akinsa ya shiga duk an chanza komai kamar ba d’akin nasa ba, akwati ya bud’e ya d’auki towel ya d’aura sannan ya nufi toilet domin yin wanka, Bayan ya fito ne yaga an ajje masa manyan kaya a bisa gado yay murmushi yasan ba aikin kowa bane sai Alhjinsa saboda shi bai cika son ganin babban mutum ya saka qananan kaya ba,a cewarsa basu masa kyau,jikin nasa ya fara feshewa da body spray sannan ya murza mai ya d’auki shaddar dake visa gadon ya sanya ya ya fesa turare sannan ya d’auki wayarsa ya fita. Ba qaramin mamaki yayi ba ganin Aminan nasa har sun iso duk sun zauna bisa table tare da iyayen nasa,shi kad’ai ne ake jira,yana qarasawa ya miqa masu hannu suka gaggaisa tare da murnar sake ganin juna cikin qoshin lafiya. Salim,Salman da Umar Abokanansa ne tun suna karatu a America sai dai su tunda suka qare karatun suka dawo gida sakamakon shi da saida ya fara aiki a Asibitin chen qasar. Salman d’and’an babban malamin garinne tunda suka dawo yaqi aikin gwamnati ya kama kasuwancin saida kayan mota,komai kake so da ya danganci mota idan har kaje kamfaninsa ka samu ka gama,har fenti suna yi ma mota,kuma suna sayen tsohuwa, Salim mahaifinsa babban d’an kasuwa ne dake kasuwancinsa tsakanin qasashen duniya,ya jima da rasuwa a hanyarsa ta dawowa gida daga Morocco sukay had’arin jirgi,salim shi kad’ai ne d’ansa a duniya sai ko mahaifiyar salim d’in, sai ya kasance tunda mahaifinnasa ya rasu yawancin dukiyarsa ta dawo hannunsa daganan ya yanke shawarar bud’e super market’s kuma yakan d’an ta6a aikin asibiti, Sai Umar wanda shi mahaifinsa d’an siyasa ne har gwamnan garin nasu yayi,tunda ya dawo gida ya soma aiki a Federal Medical Center dake cikin jahar tasu ta Katsina,don shi dama burin nasa bai wuce yayi Aikin gwamnati ba, Dukansu su hud’un Kansu a had’e yake tunda suka isa qasar ta America, a gidan mahaifin Marwan suke zaune har Allah Yasa suka qare karatun suka yo gida suka bar Marwan d’in a chen.. *Hawwa Damary* [10/11, 4:19 PM] Hawwadamary : *MARWA DA MARWAN.* 9 *~By Hauwadamary* (NWA) Dedicate to *Memxiey_fulla * Shima zaunawa yay kusa da su suka shiga hirar yaushe gamo,Marwa wacce tunda ya shigo take satar kallonsa Amma shi hankalinsa baya gurin da alama ma bai lura da ita ba,gani tay idan ba tayi magana ba hankalin nasa baxai yo kanta ba yanda suke ta zuba hira da abokansa, daurewa tayi ta gaishe shi,ya juyo ya Amsa mata da fara’a a ransa ko mamakin kyaun da ta qara yake sai yaga a hoto ma baiga komai ba,murmushi ya qara yace”gaskiya yarannan kun girma sosae,yanzu Marwa ce ta zama haka? Kamar ba ita bace lokacin da na tafi ko rarrafe bata yi ba” Firdau tace”haba yaya wane irin bata rarrafe,lokacin daka tafi fa tayi wayau har ta fara zuwa school” Yace”oh,kinga na manta ni,tou gaskiya na manta” ya kai dibansa ga Hassana da Usaina wad’anna keta faman cin Abinci ba ruwansu, yace”Gaskiya Hjy y’an biyun nan naki sun fiye cin tsiya,shiyasa gasu nan tubarkallah,idan ba Wanda ya sani ba sai yace sun girmi firdau” Hajiya tace”ba abunda ya shafeka ae saida lafiya ake ci,saboda haka a daina sa ma y’an biyu na ido” Duka gurin suka sa dariya harda su Alhj, haka suka cigaba da cin Abincin cikin raha,bayan an qare ne kowa ya shiga miqa masa gift d’insa,Alhjinsa,Mai daloli,Umma da Hajiya ginin gida suke yi masa,sai salim daya bashi mota Mercedes Benz,shi kuma salman ya d’akko masa Akwati cike da Manyan kaya masu tsad”a ya miqa masa yace a kwashe na turawa a kyautar,umar kuma dangin su hula,agogo da takalma ya bashi masu uban yawa,sai qannen nasa kowa da tashi, saboda farin ciki kasa magana yayi sai hawaye, sai magrib kowa ya tafi gida,Mai daloli ma da iyalansa suka tafi, koda ya koma d’aki gift d’in da Marwa ta bashi ya d’auko ya shiga bubbud’ewa a ransa yana jin qara qaunarta, Bayan dawowarsa da sati biyu ne Alhjinsa ya kirasa yake tambayarsa batun Aiki, yace,shi gaskiyar magana baya sha’awar yin Aiki a Nigeria,da shi shawarar da yake zai bud’e kamfanin saida motoci ya rinqa shigowa dasu daga America, Alhjin nasa yace”banqi ta taka ba,Amma inaso ka sani sana’ar saida motoci yana buqatar kud’i sosae” Yace”Alhj ay wannan ba matsala bace inada 3billion da y’an kai a account d’ina ko dasu ne sai na siyo y’an madaidaita kafin Allah Ya bud’a” “Tou shikenan,sai ka d’auki 1billion a Account d’ina ka qara idan naga ina da wadatattun kud’i zan sayi fili nasa a soma ginin kamfanin” Yace”Nagode Allah Ya qara girma da d’aukaka” Yace”Ameen don rabbil izzati,sai kaje ka samu Mahaifiyar taka ka shaida mata yanda mukayi kasan sha’ani na mata tana iya cewa ba’a sanar da ita ba” Yay dariya yace”zanje insha Allah,yau ma tace ni zanje d’auko ta gurin Aiki” “Tou Madallah,ae saika hanzarta naga qarfe shiddan ta kusa yi” “Tou Alhaji” ya fad’a cikin ladabi sannan ya fita. Abunka da masu abun,ba’ayi wata da maganar ba aka gama ginin kamfanin,komai yayi tsari kamar a qasar waje,cikin sa’a ya shigo da motoci masu masifar kyau,y’an ubansu wad’anda sai wane da wane zasu iya hawa, An saka ranar asabar da lahadi za’ayi saukar qur’ani a gurin Wanda harda Marwan da Abokansa za’ae,sai kuma ranar litinin ayi taron bud’e kamfanin mai suna MARWAN MOTORS COMPANY NIG L.T. Ranar da suka gama sauka ta qarshe da daddare ya shirya domin ya kai ma Ummansa ziyara don tunda aka soma hidimar gini bai samu ya leqa ba sai dai sukanyi waya akai-akai. Shirinsa ya gama cikin wani yadi brown mai tsada duk cikin kayan Salman ne ya d’auko hula wacce tayi shige da yadin nasa ya sanya sai ya d’aura agogo ya qara fesa turare sannan ya d’auki key d’in motar da Salim ya basa, ba qaramin so yake yi ma motar ba dama duk kayan da aka basa. Horn d’aya yayi Iro mai gadi ya leqo,ganin ko waye yasa yay hanzarin fitowa ya bud’e masa yana fad’in”barka da zuwa ‘yalla6ai” A taqaice ya qamsa gami da zaro dubu biyu ya miqa masa,yayta zuba godiya. *Hawwa Damary* [10/11, 4:19 PM] Hawwadamary : *MARWA DA MARWAN.* 10 ~*By Hauwadamary* (NWA) Dedicated to *Memxiey_fulla * A harabar gidan yaci karo da Mai daloli yana qoqarin shiga mota,cikin Azama ya qarasa inda yake ya duqa har qasa ya gaishe shi, ya Amsa gami da tambayarsa y’an gidan,yace”suna nan lafiya sunce a gaishe ku” Yace “tou Madallah,ae chen gidan na nufa yanzu shi Alhajin yayo man waya yace yana son ganina nasan bai wuce maganar kamfaninka,gobe ne za’ayi taron bud’ewar ko?” Yace”eh,da qarfe goma na safe Insha Allah” “Allah ya nuna mana” Yace”Ameen”daganan ya qarasa ciki,Marwa ce kad’ai a parlour kwance tana kallo a system d’inta,jin sallamarsa yasa tayi saurin tashi tsaye tace”laaa yaya dama kana tafe shine baka fad’a man ba” Yace “dama so nake nayi maki zuwan bazata,kuma da alama kin razana” Tay dariya tace “sosae ma” daganan ta gaishe shi,yace”naqi na Amsa tunda baki murna da ganina ba” “Wallahi yaya nayi murna da ganinka sosae ma” Yad’an duqo ya d’aga mata gira yace”da gaske?” Tayi murmushi tace”da gaske mana” “Tou na yarda,ina Ummana take?” Ya tambayeta yana d’an waige-waige, Tace”yamzu ba dad’ewa ta hau sama tace kanta ke ciwo zata d’an kwanta Amma bari na tado ta” Yay saurin cewa”a’a,ba sai kin tado ta ba,zan jirata har ta tashi, ita kuma y’ar umman ta taya ni hira ko?” Ya qarashe maganarsa yana kallonta, bata ce komai ba ta sadda kai qasa tana murmushi, Yace”yawwa bani labarin qawayennan naki figaggunnan wad’anda na ganku rannan a gida” Tace”memxy da kuluwa?” Yace”ni ya za’ay na San sunansu, wad’annan dai masu shegen surutun,har gara ma mai y’ar qibar naga ita tana da d’an hankali” “Kuluwa kenan,Amma yaya ai itama memxyn tana da hankalin” Yay dariya yace”dama haka zaki ce,wai me kukayi ne a gidan ni yunwa nake ji,gashi ko ruwa ma baki kawo man ba” Tace”ayi man haquri bari naje na kawo sai na zubo maka abincin daga nan”ta miqe Har tayi nisa ya kirata,ta juyo yace”menene kuka dafa?” Tace”jallof cous-cous ne sai pepper chicken” “No,bani son cous-cous dora man spaghetti sai ki had’o man da pepper chicken d’in” Tace”tou”daganan ta miqe ta nufi kitchen shi kuma ya kwanta bisa 3seater ya d’auki system d’in tata ya cigaba da kallon, Baifi minti goma ba yana kallon,memxy da kuluwa suka shigo da hayaniya suna qwala ma Marwa kira tazo ta raba masu wata gaddama wai da Enrique Gil da yaron da yay The promise (pangako sa’yo) wa yafi kyau,ita memxy tace Enrique yafi kyau ita kuma kuluwa tace Angelo yafi,shine suka nufo gurin Marwa ta raba gaddama, ‘Dakin Marwan suka nufa ba tare da sun lura da wata halitta dake zaune a gurin ba *Hawwa Damary* [10/11, 4:19 PM] Hawwadamary : *MARWA DA MARWA*. 11 *~By Hauwa Damari* (NWA) Dedicated to *Memxiey_fulla * Sun Shiga d’akin nata basu iske ta a ciki ba don haka suka qara kwaso gaddamarsu suka nufo parlour, dukkansu turus sukayi lokacin da sukay ido hud’u da Marwan ya had’e girar sama da ta qasa,kuluwa ce ta fara yin hankalin gaishe shi sai memxyn ya Amsa fuskarsa ba yabo ba fallasa a dai-dai lokacin umma ta sakko tana fad’in”hayaniyar me nake ji ne tun d’azu haka?” Memxy tay karaf tace”Umma kuluwa ce wllhy” Kuluwa ta zabga mata harara tace”eh lallai ma,ni da ke waye ya fara gaddamar” “Tab,aje a tambayi mami(maman kuluwa) ae a gabanta aka fara” memxy ta fad’a tana hararar kuluwan itama da gefen ido Umma tace”duk wannan bata taso ba,yanzu dai ku wuce gurin y’ar uwar taku ta gaddama sai kuy tayi,daganan Ku turo man ita” Sukace sun diba basu ganta ba,tace su diba kitchen,suka d’ugunzuma sukayi kitchen d’in. Girgiza kai kawae umma tayi kafin ta fuskanci Marwan tace”tun dazu ka shigo ne?” Ya d’an sosa kai yace”eh to,ban wani dad’e sosae ba,Marwa tace man kin d’an kwanta ne baki jin dad’i” Ta d’anyi tsaki tana shirin zama tace”wallahi wani matsanancin ciwon Kaine nake fama da shi nafi 2yrs,idan na fara kaina kamar zai tsage” “Innalillahi,gaskia ciwon kai baya da dad’i ko kad’an,tou akwai maganin da kike sha ne? Tace”i toh da dai panadol extra nake sha…” Ya katseta”haba umma kawai baki je asibiti sun diba ki ba sai ki rinqa shan qwaya,qila ma wannan baiyi dai-dai da ciwon kan da ke damunki ba,zan turo maki Dr Umar ya diba ki idan Allah ya kaimu gobe da safe,amma don Allah umma ku daina shan wannan maganin” Tay murmushi”to insha Allah” daganan Marwan ya gaisheta ta amsa tare da tambayarsa y’an gida,suna cikin haka Marwa ta shigo hannunta d’auke da tray ta zo ta dire a gabansa ta juyo gurin qawayenta,Sam ba haka Marwan yaso ba,shi idan da ason samunsa ne ta zauna yana ci suna hira,Amma ba yanda ya iya dole ya haqura. Sai gab da magrib prayer ya baro gidan,kai tsaye gidansu ya nufa,tun data harabar gidan ya soma karo da motar Mai daloli,saboda haka sai kawai ya nufi parloun,bayan ya zauna ya qara gaishe su,Alhajinsa yace”dama yanzu maganar ka muke sai kuma gaka ka iso” ya gyara zama sannan ya cigaba”dama ba wani Abu bane ni da Mai daloli munyi magana ne akan tarewarka sabon gidanka munga gaskia ya dace ace tare da abokiyar zama ya kamata ka tare,don yanda tarbiya tayi qaranci a zamanin nan,saboda haka idan kana da wacce tayi maka yanzu sai ka Sanar da mu a san abunyi” Yay qasa da kai yana d’an murmushi cike da jin kunya, shi yanzu ta yaya zai iya Sanar da su marwa ce za6in ransa,kai gaskia abun da kamar wuya,dama Alhajinsa ne kad’ai da da sauqi… Shirun da yayi ne yasa Mai daloli fad’in”kai fa muke saurare” “Um…dam..a um Marwa c…” Tun kafin ya qarasa yaji Alhajinsa ya sama fad’in”Alhamdullh,kaga abunda nake fad’a maka ko”ya kalli mai daloli yana dariya irin tasu ta manya,shima Mai dalolin dariyar yake, A nan take suka shirya komai aka tsayar da rana sati ukku masu zuwa,Alhajin Marwan yace sai anji ta bakin ita yarinyar kada ayi mata dole,Mai daloli yace,ay aure kamar anyi an gama ne,ba wata maganar tambayarta, tou da haka suka tashi a ranar kowa da farin ciki,musamman ma Marwan da yake ji kamar anyi masa kyautar rai. Ko da sauran Y’an uwa suka ji ba qaramin farin ciki sukayi ba kar ma dai umma taji,kai tsaye shirye-shirye suka fara ba kama hannun yaro kasancewar an saka qurarren lokaci. An sake gyara gidan da Amarya zata zauna anyi jere na ubansun kaya daga sama har qasa kasancewar mai bene, Ana saura sati d’aya biki aka kawo lefe na gani na fad’a ga mota irin wacce y’ay’an masu hannu da shuni ke yayi a wannan zamanin.. *Hawwa Damary*e a reply [10/6, 12:39 PM] Hawwadamary : MARWA DA MARWAN. 12 ~By Hawwa Damary (NWA) A wannan hidimar shirye-shiryen ta biki ce Allah ya had’a jinin Dr Umar da kuluwa,cikin qaramin lokaci magana tayi qarfi da yake Umar d’in yace ba da wasa yazo ba,an sanya bikin su wata biyu bayan na su Marwan. Memxy baki har kunne qawayenta zasuy aure ta samu gurin zuwa,har lissafi take yau idan taje gidan Marwa gobe sai taje gidan Kuluwa,ko kuma idan ta shafe sati tana zuwa gidan wannan d’ayar ma haka,su duka sukanyi dariya suce,ke kuma da yake zamanki kenan ba zaki aure ba. Musamman Umma ta aika nijar aka d’auko mata Hafsat mai Amare domin gyaran amarya,tun ranar da ta zo ta shiga gyaran amarya aka kulle ta a d’aki ko parlor ba’a barinta fita sai dai a shigo gurinta,shima d’in daga qawayenta sai Umma da ita Hafsat d’in,ko da wani Abu take so sai dai tayi waya a kawo mata, wannan abu ba qaramin takura ma Marwan yayi ba,don shi baiqi ace kullum yana manne da Amaryarsa ba. Biki ya rage saura kwana biyu a d’aura aure,tun daren jiya Marwan ya kasa sukuni burinsa kawae yaga yayi tozali da abar qaunarsa don haka tunda ya dawo masallaci sallar Asuba bai koma ba yay shirinsa ya bar gidan,kai tsaye gidan su Marwa ya nufa,mai gadi na ganinsa ya bud’e masa gate yana gaishe shi,hannu kawae ya d’aga masa don gani yayi idan ya tsaya yi masa magana mutanan gidan na iya jiyo sa, Da sand’o ya nufi d’akin Marwa a lokacin tana zaune bakin gado idar da sallarta kenan ta d’auko waya da niyyar kiransa sai ganin mutum tayi ya turo qofa,ba qaramin razana tayi ba sauqin ta ma Hafsat ta shiga toilet amma duk da haka sai da ta kai dibanta hanyar qofar toilet d’in. Sororo yayi yana kallonta ta chanza masa kamanni gabaki d’aya kamar ba ita ba har wani yellow yellow take yi ga sheqi tana yi tayi bul-bul kamar ka ta6a jini ya fito,gaskia ba don a d’akinta ya ganta ba da bazai iya ganeta ba don gabaki d’aya kamanninta ya chnaza. Ganin baya da niyyar magana kuma ta tabbata Hafsat gab take da fitowa yasa tay saurin gaishe da shi, Ya had’e fuska yace”naqi na Amsa,haka ake gaisar da miji a garinku”ya qarashe maganarsa yana qoqarin zama a bakin gado,ta zaro ido tace”yaya don Allah ka rufa man asiri ka tashi kada azo a ganmu” “Laifi nayi don nazo ganin matata,nifa na gaji da 6oyonki da akeyi don wallahi ba qaramar wahala nake sha ba,saboda haka zo nan ki zauna kallonki nazo yi” ya nuna mata kusa da shi. Murmushi tayi ta zo ta zauna,ya tsura mata ido kamar zai lashe ta,wata matsananciyar kunya taji ta kamata,sunfi qarfin minti biyu a haka,sauri tayi ta miqe don tunowa da tayi da Hafsa, ta marairaice fuska kamar zatay kuka tace “pls mana yaya kar a ganmu,kaje zamuyi waya” Yace”tou shikenan my princess zan dai tafi ba don na gaji da ganinki ba my beautiful durling, I love u” ya sakar mata sumba a goshi. Tay murmushi kawai cike da jin kunya. Ya dafe kai yace”gaskia dole ne nayi maganin wannan kunyar don da alama ni zata cuta” Ta qara yin murmushi,har bakin qofa ta raka shi ta dawo,tana zama hafsat ta fito ta sauke ajiyar zuciya, Hafsat tace”naji kamar kina magana ko Hajiya ce ta shigo?” Tace”a’a Abba ne ya zai fita shine ya biyo ya bani saqo”hakanan ta samu kanta da shafto qarya, “Nifa ince sai naji kamar muryar namiji” “Un” kawai ta iya ce mata saboda ta lura idan ta cigaba da biye ma Hafsat to lallai sai ta karto ta. Washegari y’anmatan Amarya sukay kamu a nan harabar gida su Memzy,kamun da ya Tara y’ay’an manyan Attajiran katsina da kewayenta,wad’anda duk yawanci tare sukay makaranta a Ulul-Albab. Ranar Asabar da misalin qarfe biyu na rana aka d’aura auren MARWAN MANSUR SAMBO da amaryarsa MARWA SALMANU MAI DALOLI akan sadaki dubu hamsin lakadan ba ajalan ba,mutane fiye da dubu ne suka shaida haka, A dai-dai lokacin Marwa ta kulle kanta a d’aki tayi nafila raka’a biyu ta shiga zuba addu’o’i da fatan Allah ya basu zaman lpia da zuri’a d’ayyiba, tana cikin haka ne taji gud’a ta karad’e ko ina a gidan sai kawai ta fashe da kuka shikenan ita yanzu ta zama qarqashin inuwar wani ba iyayenta ba, Nan abokanan wasa da y’an uwa suka rufeta da tsokana. Ranar tasha nasiha sosae gurin iyaye,wannan yayi,wannan yayi har ta soma gajiya, Anayin sallar la’asar Abbanta yace a fito da ita a kaita d’akin mijinta,aifa nan sabon kuka ya tashi ta qanqame Umma tana ta faman yi kamar ranta zai fita, da qyar aka samu aka raba su, Barhim estate a nan gidan nata yake sai ddai ya banbanta da irin tsarin gidajen,hawa biyu ne gidan,fentin brown sai aka ratsa milk,tun daga waje zaka fara karo da fulawowi masu kyau da qamshi. Ana yin sallar magrib sauran y’an kawo Amarya suka watse ya rage daga Amarya sai Aminanta kuluwa da memxy…….. [10/7, 10:09 PM] Hawwadamary : [10/7, 9:48 PM] Hawwadamary : *MARWA DA MARWAN* 13 ~Hawwa Damary (NWA) Dedicated to *Memxiey_fulla* *CIGABAN LABARI* Bayan ya dawo rakiya Abokannasa kai tsaye inda ya barta ya nufa lokacin qarfe tara harda minti sha biyar na dare. Zaune take a bisa gado ta yi tagumi,har ta qarasa ya zauna bata San ya shigo ba yasa hannu ya zame tagumin da tayi ya had’e fuska yace”tunanin me kike yi haka har na shigo baki sani ba,sai kinja wata lalurar ta sameki ko saboda kinga ba ke keda asara ba” Tay murmushi tace”wallahi yaya ba haka bane,kawae dai ina tunanin su umma ne” Cikin dariya yace”tou ko in tashi in kaiki ne?” Itama dariyar tayi tace”ni dai bance ba yaya,kawai dai bazaka gane bane” “Zan gane mana,bari dai na gama cika cikina sannan” ya d’an shafa cikinsa”kinsan rabona da cin abinci tun breakfast, tashi kije freezer dake kitchen akwai wata leda zaki ga kaza ce ciki ki d’auka kiyi mana warming d’inta,oh sorry Ashe Amarya ce ke ko,na manta Amarya bata aiki,tashi muje tare sai ki taya ni hira ni inyi aikin” Tay dariya tana qoqarin miqewa,tace”kai dai kawae zauna ka huta waye ya ce maka amarya bata aiki? Ai ko bata yi ni dai zanyi ma yayana” Har cikin ransa yaji dad’i kuma ya tabbatar marwansa na qaunarsa kamar yanda yake qaunarta,shima tashi yayi ya rufa mata baya, lokacin da ya isa har ta juye a plate ta saka a cikin warmer,bayan sun gama suka zauna a dinning table suka ci tare da korawa da sanyayyar youghurt,lokacin qarfe goma saura minti shidda. Bayan sun kammala suka nufi parlour suka kunna kallo suna yi,amma gabaki d’aya ba fahimta take ba saboda ita ba ma’abociyar son qwallo bace,duk ta gaji burinta kawae ta ganta a bisa gado tana bacci. Lura yayi da yanayin da take ciki ya tashi ya kashe komai da kallo sannan ya zo ya d’auketa chak bai dire ta a ko ina ba sai bedroom d’inta bisa kujera,ya ajjeta yana qoqarin su had’a ido,amma taqi,cikin muryar mai taushi yace”my prncss ki tashi muyi sallah muyi ma Allah subhanahu wa ta’ala da ya kawo mu wannan lokacin da muke zaune a qarqashin inuwa d’aya” “Tou yaya,ka tafi to sai na tashi” cewar Marwa Dariya yayi ba tare daya ce komai ba ya fita tare da ja mata qofa, Sanyayyar ajiyar zuciya tayi tare da miqewa ta nufi toilet ta watsa ruwa tare da d’auro alwallah, a tsanake ta gama shirinta sai qamshi take zubawa, Har ta d’an zauna bakin gado sai gashi ya shigo sanye da jallabiya fara shima dai qamshin yake zubawa, Da murmushi d’auke a fuskarsa ya qaraso inda take,dama already ta sanya hijab sai ta miqe kawae,shima ba tare da 6ata lokaci ma ya tada masu, Sun dad’e suna addu’o’i na neman zaman lafiya da zuri’a d’ayyiba,bayan sun gama wannan ya dafe kanta ya shiga karanto addu’a kafin daga bisani ya yi mata y’an tambayoyi da suka shafi addinin musulunci,kamar su wankan tsarki da dai sauransu,tiryan tiryan ta Shiga zayyana masa ba tare da wata gargada ba duk da wani nauyinsa da take ji. Ta matuqar burgeshi kuma har ga Allah ya ji dad’i ko ba komai ya za6a ma y’ay’ansa uwar da ta chanchanta, agogo ya kalla qarfe sha biyu da minti biyu don haka suka soma haramar bacci. Wannan dare a garesu dare ne mai d’umbin tarihi wanda ke cike da faranta ran juna sai dai ga y’an uwansu da abokan arziqi wannan dare shine yafi ko wane dare muni a cikin rayuwarsu, ta d’an tsagaita tare da goge hawayen da ya soma taruwa a idonta, Duk da nima jikina ya soma yin sanyi hakan bai sa na lallasheta ba don bansan me ke sanya ta wannan zubar hawayenba,sai dai ba qaramin zaquwa nayi ba da son jin abunda ya faru a Daren. Maimakon naji ta cigaba da bani labari sai naga ta miqe ta nufi hanyar kitchen, jim kad’an sai gata ta fito hannunta d’auke da tray cike da drinks bayanta kuma Lantana mai aikinta ce itama d’auke da qaton tray na manyan warmers,duk kusan a tare suka ajje kafin Lantana ta juya ta fita,ita da kanta matar tayi serving d’inmu. “Ikon Allah” na fad’a a raina saboda ganin wasu irin abubuwa da aka had’a a abincin wad’and’a tunda nake a rayuwata ban ta6a ganinsu ba,aifa ban tsaya nuna baqunta ba na saki ciki na nad’i abincinnan saboda idan na bar gidan bansan lokacin da zan qara gani ba balle har na ci,”kai gaskia yau idan na koma gida sai y’an gidanmu sun gaji da labari,wallahi harda qarya zan had’a masu duk don labarin ya qara dad’i” nay ta wannan saqe-saqen cikin raina. Bamu cigaba da labari ba saida muka gabatar da sallar azahar sannan muka zauna ta kalleni da murmushi tace”tou Hajiya Hauwa Damari a ina muka tsaya?” Nayi saurin cewa”a lokacin da suka kwanta donyi bacci” Tayi dariya sosae tace”Ashe dai baki da mantuwa” Nima dariyar nayi nace”ay wannan qaton kan nawa ba banza yake ba” Dariya ta qara yi tace”ay naga Alama,Bari dai na cigaba maki kafin yara su dawo” Nace”ay lallai kam Tayi murmushi sannan ta cigaba kamar haka………. *Hauwa Damary* [10/9, 11:04 AM] Hawwadamary : [10/9, 10:02 AM] Hawwadamary : *MARWA DA MARWAN*. 14 ~*Hawwa Damary* (NWA) Dedicated to *Memxiey_fulla* Basu suka sami natsuwa ba sai qarfe ukku da rabi da minti biyu na dare, rungumeta yayi a jikinsa zuciyarsa cike da farin cikin da bai ta6a yi ba tunda ya zo duniya,kai gaskia Allah na sonsa da ya shigo da Marwa a rayuwarsa har ta zama matarsa,ya lalubi dai-dai saitin kunnenta yace”I love u my prncss,I love u with all my heart nd I promise to be with u forever and forever moree” Tayi murmshi tare da qara shigar da kanta cikin qirjinsa don tsananin kunyar da ya bata”wai shi yaya baisan kunyarsa nake ji ba”ta fad’a cikin ranta, fiye da minti goma suka d’auka suna jin d’umin juna kafin daga bisani ya miqe ya nufi toilet,jim kad’an sai gashi ya fito yana tsane jiki da towel da alama wanka yayi,ya kai dibansa a gurin da take tana kwance yanda ya barta ta qudundune da bargo duk sai yaji tausayinta ya mamaye sa,a hankali ya soma kiran sunanta,tace”na’am” yace”ki tashi kizo muyi sallar nafila kafin a kira sallar asuba” Ta marairaice fuska kamar zatayi kuka tace”yaya bana iya tashi” Yayi murmushi tare da matsawa inda take,baiyi wata-wata ba ya sunkuceta sai toilet,zuwan zafi ya had’a mata a cikin kwamin wankan sannan ya d’iga dettol a ciki ya sanyata ciki,ya tsaya daga gefe yana jiran ta gama,tace ita dai ya fita, yay murmushi kawae ya juya ya fita,zanin gadon dake bisa gadon ya cire duk da bai 6aci da jini ba,cikin washing machine yaje ya saka tare da kunnawa ya juya,yaso ya chanza wani sai dai yaga lokaci yana ta harararsa don haka sai ya barshi idan ya idar da sallar nafilar sai ya chanza kafin a kira sallar asuba. Wani irin matsanancin ciwon kai yaji ya sara masa a gefen kansa na dama,yay saurin dake kan yana karanta addu’a,sai kuma yaji ya lafa masa don haka ya tada sallarsa,ya duqa da niyyar yin sujjada kenan ciwonkai ya dawo sabo na yanzu ma yafi na d’azu don duka kanne ya d’auki zugi. Sai da ta gama komai tsaf ta d’auro alwallah sannan ta fito,ganin sa a sujjada yasa ta soma sauri don kar yay ta kiranta,doguwar riga kawai ta zura sannan ta d’auko dogon hijab d’in da ta d’inka musamman don yin sallah ta sanya,har lokacin bai d’ago daga sujjadar da yayi ba,hakan yasa ta nemi guri ta zauna a bakin gado tana jira ya idar su yi nafilar da ya ambata,ta diba agogo lokacin qarfe hud’u saura minti biyu. Sai dai abunda ya bata mamaki bai wuce ganin har yanzu bai d’ago ba kawo yanzu ta fara tsorata da wannan sujjadar tasa,a hankali ta soma kiransa sai dai shiru. Gabanta na fad’i ta qarasa gurinsa tasa hannu ta d’an ta6a sa sai yay luuuuu ya fad’i,a rud’e ta d’auki Hannun sa ta d’auka ta saki sai ya fad’i yarab ga jikinnasa yayi sanyi qalau,a gigice take fad’in”innalillahi wa inna ilaihirraju’un”ta soma jijjiga shi tana kira”yaya don Allah ka tashi bana son wannan game d’in,please yaya ka tashi”tana yi tana kuka kamar ranta zai fita”yaya ka manta Al-qawarin da ka yi man na zaka zauna da ni har abada,please yaya ka tashi mu cigaba da zama har abada”amma yaya ina, rai yayi halinsa,Allahn da ya yi sa ya amshi kayansa,rayuwa kenan,yanzu-yanzu kake da mutum yanzu-yanzu ace maka bashi,duk wani mai rai sai ya d’and’ani mutuwa,walau ta hanyar hatsari ko rashin lafiya ko farat d’aya dole ne a mutu,yanzu ga Marwan bai ta6a kawo ma ransa a cikin darennan zai rasu ba sai gashi lokacin sa na cika ko second d’aya bai qara ba,kullu nafsin za’ikatul maut,haqiqa duk wani mai rai mamaci ne,sai dai muyi fatan mu cika da kyau da imani. Iya rud’ewa to Marwa ta rud’e fiye da zaton mai karatu,iya gigicewa ta gigice,wayarta ta shiga laluba don ta kira umma ta sanar da ita halin da ake ciki sai dai kash ta manta a parlourn qasa ta manta wayar ta shiga laluben tasa sai dai harta karad’e ko’ina bata ganta ba,duk ta bi ta rikice lokaci kad’an ta chanza kamar ba ita ba,gudu-gudu sauri-sauri ta dinga had’awa harta sauka qasa,tayi sa’a wayar tata na bisa kujera don haka batay wata-wata ba ta soma kiran number Umma saidai har ta qaraci ringing d’inta ba’a d’auka ba,ta kuma kira shima ba’a d’auka ba,a taqaice saida ta kira yafi sau goma ba’a d’aga ba dole ta haqura ta shiga neman number y’an gidansu Marwan sai dai duk wanda ta kira number a kashe,ita sam ta manta saran y’an gidansu na da zarar goma tayi suke kashe waya,ta d’ora hannu a kai abun duniya duk ya taru yay mata yawa, memxy ce ta fad’o mata a rai aiko batay wata-wata ba ta danna mata kira,lokacin memxy na tsakiya da bacci mai cike da mafarkin Salim,cikin bacci taji wayarta na ringing tay banza da ita,aka kuma kira a karo na biyu tayi tsaki gami da janyowa,my lady ta gani a screen d’in tay saurin d’auka cikin gigin bacci tace”shegiya me zaki man ne kika wani daman bari sai anjima na kiraki”qit ta kashe wayarta ta tare da ta saurari abunda zata fad’a mata ba, “Na shiga ukku” ta fad’a tare da qora hannu saman kai,ta nufi kanyar komawa sama,step biyu ya rage mata ta tuna da baba mai gadi,juyowar da zatay keda uwa ta take dogon hijabinta ta baya,nan ta fad’i ta cigaba da gungure har ta isa qasa,take ta suma jini ya soma zuba ta kai,hanci da baki. Baba maigadi ya fito zai kama ruwa a bayinsa da ke wajen d’akinsa yaji kamar qarar fad’uwar wani abu,sai bai kawo ma ransa komai ba,da yake yayi dai-dai da soma kiran sallah a masallacin dake wajen gidan,sai kawae ya d’auka irin qarar nan ce ta kunna loud speaker,don haka sai yay sauri ya kama ruwa yay alwallah sannan ya nufi masallaci.. [10/11, 9:12 AM] Hawwadamary : [10/11, 7:56 AM] Hawwadamary : *MARWA DA MARWAN* 15 ~*By Hawwa Damary* Dedicated to *Memxiey_fulla* Marwa ce kwance cikin jini tana miqo mata hannu Ta taimake ta gefe guda kuma Marwan ne tsaye yana hawaye yana kallon gefen da Marwan take kamar yana son sanar da ita wani abu sai dai ya kasa, kafin ta kaiga qarasawa gurin Marwan tuni ta fad’i sumamma,6at Marwan ya 6ace daga gurin da yake tsaye, firgigit ta farka tana fad’in”innalillahi wa inna ilaihirraju’un”tare da dafe qirji,gaskia ba qaramin kad’uwa tayi ba da wannan mafarkinnata,hakanan sai taji hankalinta bai kwanta ba,haka burinta bai wuce ta san halinda y’ay’annata suke ciki ba,ta kalli agogo qarfe biyar saura kwata,kuma a dai-dai lokacinne aka soma kiran sallah a masallacin unguwarsu. Tashi tayi ta shiga toilet ta d’auro Alwallah ta gabatar da sallar Asuba gabanta na fad’i akai-akai. Bayan ta idar ta d’auko wayarta don ta kira mijinta taji yanda ya kwana kasancewar tunda aka fara hidimar biki bata samun zuwa d’akinsa ta kwana, 11 missed calls ta gani daga Marwa,nan take ta danna kira amma har ta qaraci ringing ba’a d’aga ba ta,sai da ta kira sau hud’u ba’a daga ba,abunka ga mai saurin shiga rud’u duk sai tabi ta rud’e ta figi hijab tayi hanyar d’akin mijinnata,taje a sa’a don a dai-dai lokacin ya dawo masallaci,yana ganinta face”lafiya?” Tace”inafa lafiya”nan ta zayyana masa mafarkin da tayi ta cigaba da fad’in”ni wallahi hankalina ba zai kwanta ba sai na dibo halinda suke ciki” Yay dariya yace”matsalata da ke kenan akwai rud’ewa,tou ki bari gari ya gama wayewa mana” “Gaskia ba zan iya bari har gari ya waye ba,don baka ji yanda nake ji ba,banqi ace yanzu na bud’e ido na ganni gidan ba”ta qarashe maganarta cikin zaquwa, yace”tou shikenan,sai ki tada audu driver ya kaiki don ban yarda kiyi driving a halin yanzu ba,kome kenan kiyo man waya,no barshi ma zan biyo bayanki nan da 15mnts idan na shirya” Tace”tou shikenan darling sai ka iso,Allah ya qara girma da d’aukaka” Ya wani lumshe ido kafin yace”Ameen matas” har cikin ransa yana jin dad’in rayuwa da ita,kullum cikin tattalinsa take shiyasa gashi nan kullum qara yarinta yake,yay murmshi a ransa yace”Allah ya barmu tare” Qarfe biyar da minti arba’in na safiyar alhamis a qofar gidan Marwan tayi ma Umma,driver nayin horn mai gadi yazo ya bud’e masa da sauri,risinawa yay ya gaisheta,ta amsa a gaggauce, Qofar da zata sada ka da parlourn gidan ta nufa,a rufe take don haka sai ta fara knocking amma shiru kake ji wai anyi wa mai dami d’aya sata. Hankalinta ya qara tashi ta kira maigadi ta tambayesa ko masu gidan basa nan ne? Yace, suna ciki tun jiya basu kuma fita ba,tsayi d’an tsaki tare da cigaba da qwanqwasawa amma har yanzu ba wani motsi,Marwan ta kira a waya gashi tana ringing amma ba’a d’aga ba,ta kalli mai gadin tace masa ya d’an samo mata abunda za’a iya 6allewa,yace”to ranki ya dad’e” ya juya ya tafi, bayan tafiyarsa ta qannan number Hajiyar Marwan,tayi sa’a ringing d’aya ta d’auka tana fad’in”kin taki sa’a don yanzu-yanzu na kunna wayar,ya gajiyar biki? Da naga kiranki baki ji yanda gabana ya fad’i ba dama yau na tashi jikina duk yay sanyi ince ko lafiya?” “Ina fatan haka d’in Hajiya,gani dai a qofar gidan y’ay’anki” ta zayyana mata mafarkin da tayi da kuma tsayuwar da take a gurin, Hajiya tace”ki kwanta da hankalinki in Allah ya yarda ma ba komai sai alkhairi,nima bari na zo gidan yanzu,Amma fa kada mu zama sirikan banza”ta qarashe maganartata da zolaya, Murmushin yaqe umma tayi tace”amma kuma a wani 6angaren ae mu iyayene,kinga haqqinmu ne mu zo muga lafiyarsu” Tace”eh tabbas! Da haka,tou sai na qaraso” Umma tace”uhmm” Ajje wayartata yay dai-dai da dawowar maigadi d’auke da gatari a hannunsa,bugu biyu zuwa ukku qofar ta 6alle,Umma ce ta soma shiga sauran suka rufa mata baya,turus tayi ta tsaya sakamakon abunda ta gani, Marwa ce kwance cikin jini face-face ba’a cikin hayyacinta ba,bata san lokacin da ta saki wayarta ba ta qarasa gurin cikin kid’ima ta rungumeta tana jijjigata,ruwa ta umarci Audu da ya miqo mata cikin fridge, yana kawo mata ta shafa ma Marwan,wata ajiyar zuciya ta saki tare da bud’e idonta da yay jawur don tsabar kwanciyar jini,bakinta ta soma bud’ewa alamar tana sonyin magana Amma ta kasa,da qyar kake gane”ma…ma…ma..” Sai kuma tayi shiru Allah kad’ai yasan azabar da take sha a lokacin,ba umma kad’ai ba harta su mai gadi saida suka zubar da hawaye, Umma tayi qarfin halin cewa”ina Marwan d’inne ya barta cikin wannan halin”ta kalli mai gadi. Yace”wallahi Hajiya bansan inda yake ba,ni dai rabon da naga wani ya fita gidannan tun jiya da daddare” Ta qaure fuska tamau tace”kana nufin Marwan d’in na ciki wannan Abu ya samu Marwa? Zancen banza zancen wofi,” ta kai dibanta ga Audu tace”kama man ita mu kaita asibiti” Sai dai ita Marwa har yanzu qoqarinta na tayi mgn ne Amma ta kasa,da qyar ta samu ta iya d’aga hannunta ta nuna masu hanyar upstairs, sai kuma ta qara yin luuuu jikin Umma ta qara Sumewa, Tsawa umma ta daka ma audu tace”ka kama man ita nace” Jiki na rawa yace”tou Hajiya” Maigadi yace”naga tana nuna hanyar saman bene ko wani abunne take son sanarw….”rufeman baki”umma ta katse shi ta hanyar daka masa tsawa,tace”shashasha Wanda baisan aikinsa ba,kana aikin meye haka ta faru da y’ata, tou ka sani baka ci bulus ba,zaka yi bayani gaban hukuma,kai kuma kamata muje”…. *Hawwa Damary* [10/11, 12:53 PM] Hawwadamary : [10/11, 9:46 AM] Hawwadamary : *MARWA DA MARWAN* 16 ~*By Hauwa Damary* Dedicated to *Memxiey_fulla* *k*ama ta yayi suka nufi mota da ita,suka sanya ta a baya umma ta zauna ta d’ora kanta bisa cinyarta sannan ta rufe,yana qoqari tada mota suka ji horn a bakin gate,mai gadi yaje ya bud’e,Mai daloli ne ya qaraso,ganinsu a nan yasa yay tunanin ko ba komai,qarasowa yay inda suke,da Marwa ya fara tozali cikin jini, yace”subnahallah me ya faru haka?” Nan umma ta labarta masa halinda suka zo suka iske Marwa a ciki, “Assha! Tou ina Marwan d’in ya shiga ya barta a haka” Cike da qosawa umma tace”ba wanda ya san inda ya nufa,yanxu dai mu fara ta lafiyar wannan d’in,sannan sai a neme sa d’azu ma na kira wayarsa baiyi picking ba” Abba ya kalli mai gadi da yayi tsuru-tsuru yace”yaushe ya fita?” Mai gadi ya shiga rantsuwa shi duk yau bai ga Marwan ba harda hawayensa, Yace”ni ba nace wani Abu bane,yanzu dai biyo ni muje ciki,Ku kuma sai Ku wuce asibitin” ya d’ebo kud’i daga aljihunsa ba tare da ya San adadinsu ba ya miqa masu ko za’a buqaci wani Abu a asibitin, Ko wane d’aki da ke a qasa saida suka diba ba Marwan,maigadi yace”yalla6ai dazu kafin hjy ta qara suma naga tana nuna sama da alama akwai abunda take son sanarwa” Mai daloli yayi d’an Jim kafin yace,su je. Gawar Marwan na nan a yanda Marwa ta barsa har ya soma sandarewa,suna shiga sukayi arba da gawar,”Innalillahi wa inna ilaihirraju’un”suka fad’a a tare,gami da qarasawa gurinnansa ba abunda suke sai sallallami,Abban ya kira alhjn Marwan d’in yace yaxo ya samesa a gidan marwan d’in,lokacin yana tare da hajiya tazo tambayar sa,ya hanata yace ba da shi ba za’ayi wannan abun kunyan, aiko tana jin wayar da aka masa tace qafarsa qafarta,yace”ay sai ki shiryo muje” tace “a shirye nake” tare suka fita lokacin qarfe bakwai da minti ishirin da hud’u. Tun daga hanya suka fara karo da jini, tun daganan suka fara shan jinin jikinsu. Mai karatu iya tashin hankali kaf dangi da y’an uwa sunga tashin hankali wanda basu ta6a gani ba,gidan biki ya koma gidan zaman makoki,ba’ay ma Marwan sutura ba sai da y’an sanda suka zo sukayi bincike tare da lokitoci suka gano ba abunda ya ci ko ya same shi kawai dai ikon Allah ne wanda baya wuce ranarsa. Qarfe hud’u aka yi jana’izarsa aka kaisa gidansa na gaskia,gidanda duk wani mai rai dole ne ya je shi, Kawo yanzu kuka yaci qarfinta,bama ita kad’ai ba har ni da nake zaune tana bani labari,ba mai lallashin wani idan ka ganmu a lokacin sai ka rantse da qur’ani a yanzu ne akayi mutuwar. Ta cigaba cikin kuka”wallahi Hauwa’u tashin hankali an shigeshi fiye da yanda kike tunani, duk wani wanda yasan Marwa da Marwan ya tsorata da wannan al-amarin karma abokan Marwan suji, Nay saurin kallonta nace”ita Marwan fa?” Ta goge hawayen idanunta tace”Marwa na nan da ranta sai dai da halin da take ciki har gara wanda ya rasu, don zaune take bata ji bata magana,qwaqwalwarta ta had’u da jini,sai abun ya zamar mata kamar ta6in hankali,anyi maganin anyi maganin Amma ba wani sauqi sai gurin Allah,duk qasar da akaji labarin idan anje za’a dace tou anje amma har yanzu” “innalillahi,ya Allah ubangiji kaba ma baiwar nan taka lafiya,yawwa ina qawayenta memxy da kuluwa?” Sai naga tayi murmishi sannan tace”nice memxy,asalin sunana Maimuna ne,ae duk na fad’a maki a cikin labari sai kuluwa wannan kowa yasan duk Hauwa’u kuluwa ce,kuluwa ta auri Dr umar yanzu haka suna da y’ay’ansu ukku sai ni kuma na Auri salim abokin Marwan ko ince abokin fad’ana”sai dukanmu mukayi dariya,sannan ta cigaba”y’ay’anmu biyu gasu nan mace da namiji” Wai! Tabd’i jam,yanzu nan dama itace memxy,wallahi ko kad’an ban kawo ma raina ba,harma da y’ay’a,nace”Allah ya raya su” Tace”Ameen kulun majadan” Nayi dariya kafin nace”nikam cikin qasashen da aka kai Marwa anje saudiyya?” Ta d’anyi shiru alamar tunani sannan tace”gaskia ba’a je ba” Lallai gaskia mutanan mu suna tafka babban kuskure,sai lalura ta samu ayita kashe uba-uban kud’i ana zuwa qasashen arna,amma a kasa zuwa qasar saudiyya,tab! Wannan zancen duk a zuci na yi shi,a fili kuma cewa nayi”tou gaskia ku d’an gwada kaita,bari na baki misali da wani uncle d’ina,suna cikin mota zasu kano sukayi accident shima qwaqwalwarsa ta samu Matsala sosae, don a yanda kika fad’a man na Marwa sauqi ne akan nasa don abun sai ya zame masa kamar ma hauka,amma cikin ikon Allah ana kaishi saudiyya ko wata biyu basuy ba sai gashi garas,Allah Ku gwada kaita akwai nasara sosae”na qarashe ina qoqarin tashi, Tace”insha Allah zamu gwada zanyi ma umma magana,sai ki bani numbr ki nextweek idan zanje gurinta sai mu je tare” Nace”aiko nagode sosae”na Shiva karanto mata number”08067729322″ tace”tou nagode,d’an jirani na fito”ta shiga d’aki,jim kad’an ta fito riqe da babbar Leda a hannu,tace”ga cosmetics y’anmata aje ayita yi ma samari gayu” Nayi dariya nace”wane samari ga karatu,ai mu da samari sai mun fara aiki”na amsa”na gode sosae” *Hawwa Damary* [10/11, 2:44 PM] Hawwadamary : [10/11, 2:19 PM] Hawwadamary : *MARWA DA MARWAN* 17 ~*By Hauwa Damary* Dedicated to *Memxiey_fulla* Har bakin qofa ta rako ni tana d’aga man hannu,duk sai naji ba dad’a don maganar gaskia matarnan ta shiga raina sosae kuma nasan hakan bai rasa nasaba da labarin da ta bani mai ban tausayi. Gab da zan fita gate wata mota ta danno kai,wata mata ce ke ja,sai yara ciki guda biyar, biyu dai na gane y’ay’an hajiya Maimuna ne, ukkun ne dai ban sansu ba,ko da yake na manta qila matar itace kuluwa da y’ay’anta,bari in cire kalmar qila,tabbas kuluwa ce,ina lura da ita har na bar gate bata bar kallona ba. Kai gaskiya ranar y’an gidanmu sunsha labari,kayan da ta bani na zube ina nuna masu ina shafto qarya,har ce masu nayi gidan harda ginin qarqashin qasa,nace harda qofa mai magana,aiko suka rud’e idan, zan koma zasu Bini,nace”wallahi ba wacce zata Bini tayi man 6aqin cikin cin kayan dad’i”na kwashe kayana na wuce d’aki. Kamar yanda mukayi sati na cika tayo man waya tace na shirya da yamma zamu je gidansu Marwa,nayi farin ciki sosae har na kasa 6oye murna ta. Da yamma ko na shirya cikin ash colour d’in doguwar riga na d’auki jakkata na fice, a bakin gate nayi kichi6us da ita,tace”yawwa kinma hutar da ni da shiga zanyi na kiraki” Nayi dariya kawae,a mota take sanar dani gobe za’a fidda Marwa saudiyya, Nace”Amma gaskia naji dad’i Allah ya bata lafiya da zaran anje” Tayi dariyar jin dad’i tace”Ameen y’ar qanwata” Nayi mamakin ganin gidan su Marwa cike da mutane kuma duk saboda mutum d’aya suka taru,dama Ashe haka suke duk asabar da lahadi suke zuwa diba jikinta,qwansu da qwarqwatarsu, gaskia sun nuna man karamci sosae,dama ance shimfid’ar fuska tafi ta tabarma,saima da hjy Maimuna ta shaida masu nice na bada shawarar fita da Marwa saudiyya nan sukayi ta zuba man godiya harda umma harda qwalla duk sai naji kunya ta kamani, Hjy Maymuna ta jani ta kaini d’akin da Marwa take,gaskia Marwa ta had’u ba qarya,ganinta yafi labarinta kamar y’an India,tou ko ya kamannin mariganyi Marwan yake?,kamar Hjy Maimuna tasan abunda ke raina kenan ta tashi ta dakko man album d’in hotunan sa,wani shi da Marwa,wani cikin family,wasu na ranar biki,ga hoton kamfaninsa na motoci,a raina nace”Allah sarki Marwan,Allah ya kai haske cikin kabarinka.Ameen Sai yamma lis muka dawo gida,nan gidanmu hjy maimuna ta zauna da y’ay’anta har akayi isha’i suka ci abinci sannan suka tafi, Washegari litinin na koma makaranta,abun ban haushi a Daren da na koma aka sace wayata,raina yay matuqar 6achi saboda rasa number hjy maimuna da nayi,gashi ni ba gwanar welcome back ba Koda muka dawo Hutu naje gidan mai gadin yace man ay sun fi wata ukku rabonsu da gidan,gwuiwa a sa6ule na koma gida tare tsinema d’an iskan daya sace man waya. ********* Bayan shekara biyu na kammala Karatuna har an sanya ranar bikina wata biyu masu zuwa, Ranar wata litinin da yamma naji ina son zuwa shopping,Umar stores na nufa kasancewar nan na saba zuwa y’ar sayayya ta,6angaren mutanen nawa na nufa wato dogayen riguna ina d’add’aga wa,d’agowar da zanyi nayi four eyes da wata mata kamanninsu d’aya da Marwa,duk cewar sau d’aya na ta6a ganinta kuma cikin halin lalura,da yake a lokacin na tafi da tunaninta shiyasa wannan kallo d’aya nayi mata naga kamannin na Marwa,sai dai wannan na fita jiki, ina cikin tunaninnan ne har ta zo ta gabana ta wuce ban sani ba,hakanan naji ina mai son binta naga Wanda ya kawo ta,wani abun mamaki ina 6ulla kwana na ganta tsaye ita da maymuna a gurin da ake biyan kud’i.. *Hawwa Damary* [10/11, 3:26 PM] Hawwadamary : [10/11, 3:20 PM] Hawwadamary : *MARWA DA MARWAN* 18 ~*By Hauwa Damary* (NWA) Dedicated to *Memxiey_fulls* Banyi qasa a gwuiwa ba na qarasa ina murmushi,tana hango ni ta gane ni itama da murmushi a fuskarta ta qaraso ta rungumeni zuciyarta cike da murnar ganina,fad’i take”sister Ashe rai kanga rai” Nayi dariya nace”wallahi kam kedai bari,har gidanki naje aka ce baki nan” Tace”eh hakane,ai kinsan an je kai Marwa saudiyya ko?” Nace”eh” tace”yawwa bayan sun tafi da sati d’aya muma muka bi bayansu,cikin sa’a ko shekara ba muyi ba ta fara samun sauqi sakamakon kulawar da take samu daga gurin manyan likitocinsu,ga shi kuma kullum sai an gungurata anyi d’awafi da ita a shafa mata ruwan zam-zam,lokacin da muka cike shekara gaskia ta samu sauqi sai dai abunda ba’a rasa ba, a shekararmu ta biyu ne ta warke sarai kamar ba ita ba,yanzunma da kika ganmu last week muka damo shine tace na rako ta shopping”ta kalli Marwa da ke tsaye ta tsura mana ido tace”Marwa wannan itace Hauwa Damary wacce nake baki labarin itace ta bada shawarar a kawo ki saudiyya” Tun kafin maimuna ta gama tuni hawaye ya wanke mata fuska ta qaraso inda nake ta rungumeni tana fad’in”thank u,thank u sister,thank u,word can’t express my gratitude ,i really appreciat ur contribution, I luv u so much” na d’agota ina goge mata hawaye nace”don’t mention sister, I’m also glad dat u are fine now” Ta riqe hannuna muka koma ciki mukayi sayayya mai rai da lafiya,bayan mun gama kai tsaye gidansu muka wuce, Yawancinsu sun gane ni kamar zasu lasheni fadi suke dama bari mukayi mu gama hutawa sannan muje har gida muyi ma ki godiya,nace”ay ba komai” Banbar gidanba saida nasha kyaututtuka,Marwa ta badi mota mai shegen kyau irin ta yayi,mai daloli ya bani kyautar kujerar makka,hajiyansu Marwan da Alhajinsu suka bani 3million, Wohoho wa yaga Hauwa a makka,ga mota sannan ga kud’i naira na gugar naira har million ukku,ae rasa bakin godiya nayi sai kawae hawaye…….. ALHAMDULILLAH… HAKIKA MUTUWA GASKIYACE! Kuma rayuwa bayan mutuwa dole ne, kamar yanda kake rayuwa aduniya burinka kamore da mace, ka haihu, ga gidaje, motoci, kamfanoni/ kasuwanci ko aikin gwamnati. Amma fa bazaka wuce shekara 150 ba, zaka mutu. Shin? Ka tanadi abubuwan da zakayi rayuwa mai dadi bayan mutuwarka? Kokuma kana tunanin cewa babu rayuwa mai dadi ko ta kunchi bayan mutuwa? Ka tuna cewa kayi rayuwa acinkin mahaifa, zaka iya bada labari ? To haka ma rayuwa bayan mutuwa babu mai Baka labari sai Allah da manzonsa. Morewa shine ka mutu babu hakkin kowa akanka, kuma ka kasance mai bin dokar Allah. Kada ka bari idanuwanka,harshenka, kunnuwanka su jaza maka wahala bayan mutuwa. Ko zaka kiyayesu kasami rabauta? Hanyar tana cikin alqurani da hadisai,Allah yasa mu dace”Ameen summa Ameen. Anan na kawo maku wannan labari mai suna *MARWA DA MARWAN* adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *