Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, June 4, 2018

KABEER COMPLETE HAUSA NOVEL

adsense here
KABEER COMPLETE HAUSA NOVEL
[10/14, 9:51 PM] Chopy: [9/6, 17:34] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
1⃣➖5⃣

Shaharrariyar kuma kyakkyawar matashiyar yar jaridar nace da take tashe ke gafatar da program a gidan television dinsu me suna PYRAMID TV, ba wata bace face AISHA AHAMAD TURAKI. Duk wasu masoyan pyramid TV , ayanzu haka suna bakin TV dunsu suna kallon program din da take bayani kamar haka " Assalamu alaikum jama'a masu kallo kamar yadda kuke gani muna kan titin zariya Road inda muke dauko muku wanan rahoto direct daga wajen bikin bode katafaren ginin nan me suna BAGAUDA HOUSE. Kamar yadda masana sukace sunyi bincike duk 9ja ba ginin daya kaishi tsaho, sboda yana dauke da 500 upstairs a ciki, kuma ba tsawon ginin ne kawai zai birge me kallo ba, shi kanshi design din ba irinsa a 9ja. Duk manyan bakin da aka gayyata har me girma San kano yazo yanzu zuwan me girma governor ake jira.
 
     Faisal na ya kalli sagir abokina ina masifar son yarinyar nan sbd kwarewarta a aiki, tana da confidence  ga Uwa uba kyau, dariya sagir yayi sanan yace yanzu kayi magana kace kana son fitinannan kyaunta, to ka fadamata mana. Kai! Ai bazan Iya ba kasan Dan banzan kwarjini ne da ita, Amma indai da gaske kana sonta to dole kayi mata magana idan ba haka ba zakayi son maso wani,,,,,,,,,,muryar tace ta katse musu zancen da suke da cewa jama'a kamar yadda kuke gani me girma governor yazo kuma anfara gabatar da abinda ya Tara mu. Na sami nasarar ganawa da managing director na BAGAUDA trading company limited wato wato the youngest multi billionaire KABEER MOHD BAGAUDA Wanda matasa yan uwanshi ke yiwa kirari da ADON GARI, yallabai gashi yau Allah ya cika maka burinka, har ana bikin bude katafaren gininka da ba irinsa kaf 9ja, so idan bazaka damu ba pyramid TV tanaso tasan duk 500 upstairs din kayi occupying ko kuwa zaka bayar da hayar wasu? Zan bayar da hayar wasu. OK to yallabai wane irin farin ciki kake ji, kuma me zaka ce da masoyanka Wanda suka zo, da kuma Wanda suna nan a bakin TV nsu suna kallon ka? Wani lallausan murmushi yayi farin cikina baxai fadu ba sabd na Dade ina burin zuwan wanan ranar, gashi kuma yau Allah ya nunamin sbd haka tsakanina da Allah sai godiya alhamdulilla. Masoyana kuma ina mika godiyata agareku, nagode da kulawar da kuke nunamin. Wani shu'umin murmushi nayi sanan nace pyramid TV tana maka murna Allah ya sanya alkairi, shima murmushin yayi sanan yace nagode. Jama'a kamar yadda kuke gani tattaunawar da mukayi ce Mr kabeer, dafatan masoyan adon gari da basu sami damar zuwaba suna tare da pyramid TV.

     Zee ce ta saki wani ihu yehhh samira zo ki gani yau adon gari yayi smiling, dama yana murmushi? Allah ya mallaka min KB, Allah yasa shine mijina, mama ce tace a hakan kuna nade a gd kullum zaki aureshi? Kina ganin shegiyar yarinyar nan kamar wasa yanzu ba Wanda besan taba, duk wani me fada aji agarin nan sun santa, kamar yadda take gadara pyramid TV ta ubanta ce kuma haka, Amma don rashin zuciya kuna gd saidai kuci Ku kwanta, idan baki wasa ba ita ta aure Kabeer din ai, don naga alama ita yakewa murmushin. Don Allah mama dena fada kar zuciyata ta buga kinsan yadda nake son kabir kuwa?

Maman Aysha
[9/6, 20:13] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
5⃣➖1⃣🔟

Bayan an watse daga wajen taron office muka koma, muka karasa kammala wani aiki sanan na tafi. A gajiye na shiga gdn a compound na sami zee tana waya ta kalleni ta tabe baki angama yawon karuwancin an dawo? Duk rahoton da kika dakko dazu na gani, kuma naga kallon da kk yiwa KB, sbd haka idan ma sonshi kike to wallahi ki daina KB nawa ne ni kadai insha Allah ni zan aureshi. Wani murmushi nayi nace nima zan tayaki da addua Allah ya baki KB Yaya zee. Na wuce part dinmu, INA shiga na sami mum a zaune kawai saina fada kanta nace wash wallahi yau na gaji mum, ai naga rahoton da kika dauko very interest Allah ya kara daukaka min ke, amin mum ina junior da basma suna ciki basusan kin dawo ba, anje nayi wanka to kafin suzo su dameni. Mikewa nayi na shiga toilet din dakina nayi wanka nasa wata doguwar riga na fesa turare, sanan na dawo falo naci abinci, sanan junior da basma suka  dauko H/work dinsu na koya musu dad ne ya shigo aikuwa da gudu junior ya tafi ya dale shi oyoyo dad, sai kawai basma tasa kuka wai ya rigata kamota nayi haba basman aunty, rabi dashi bazan sayo mishi chocolate ba, idan da sabo mun saba da rigimarsu baka isa kayiwa daya Abu ba kaiwa daya ba. Karasowa Abba yayi ya zauna, sanan nace sannu da zuwa Abba yace yauwa Ummi na, naga aikin ki yana kyau iam proud of you Allah ya kara temakawa nace amin, sanan nayi musu saida safe na kwashi yan rigimar mum junior da basma muka shiga daki.

       Washe gari , da wuri na tashi sbd dad a part dinmu yake  suna can suna bacci da mum na tashi na hada break fast, na gyara gdn nasa turaren wuta, sanan nayiwa twins din mum wanka na shiryasu muna gama cin abinci nayi dropping dinsu a sch sanan na wuce office. Ina zuwa manaja ya kirani naje office dinsa, dama jama'a ne sun damemu akan sunaso suji matakan da Mr kabeer yabi yayi achieving goal dinsa akan ginin BAGAUDA house, shine nakeso kuje Ku same shi ya fada muku time din da zaku sami damar ganinsa, kinsan irin wanan manyan mutanen anashan wahalar ganinsu, Nace to, office dinsa zamu kenan? Eh, to bari muje. Elbash na samu yana wani aiki, nace idan ka karasa oga ya bamu aiki, wane aiki kuma? Zuwa office din adon gari, tab lalle ya hadamu da aiki kam wanan muskilin mutumin, danma dake zamu shine saukin abin, hammm in din wacece? Shifa wanan da kake gani mata basa gabanshi. Amma wallahi duk kin matansa idan ya ganki saiya jijjiga, sbd ke acikin mata daban kike, sai antara mata Dari kafin a sami guda daya irinki. Basar dashi nayi idan ka gama kayi min magana mu tafi ina office, yace is alright.

         A motata muka tafi, saida muka hau lifter sbd a hawa na 200 office dinsa yake. Ba yanda bamuyi da sakatariyarsa ba akan ta barmu mushiga Amma taki, daga karshe muka nemi PA dinsa mukayi magana dashi, sanan yaje yayi masa bayani shine yace mu sameshi ranar Saturday a gd, mukayi godiya muka tafi.
 
      Saturday 4pm
4:30 dot shine time din daya bamu, kuma PA dinsa ya fada mana baya son African time, sbd haka tun 4pm mukaje gdn muna jiran a kiramu shiru, gashi bamu karbi no PA din ba. Muna zaune har 5pm tayi nacewa elbash ko mutafi yace mu Dan kara hakuri dai, na duba naga bayan mu akwai mutane sunfi mutun goma suna jiransa. Kai gaskiya elbash na gaji mutaf.....ban karasa ba naga gate yana bude kanshi jerin gwanon motocinsa ne suka sako kai Wanda yawansu yakai guda 12 kuma duk cikinsu ba ta kasa da 3million, da gudu aka bude masa kofa ya fito, body guards dinsa suka Mara masa baya yana wata tafiya ta kasaita suka shiga ciki. Ya shiga befi da 10 minutes ba saiga PA dinsa ya fito jama'a don Allah kuyi hakuri yallabai yace ba Wanda zai Iya gani ayanzu, sabd ya dawo agajiye yana bukatar hutawa, sbd haka don Allah kuyi hakuri zan karayiwa kowa sbn schedule na ganinsa, wasu daga cikin Mutanen sukace ba matsala, cikin bacin rai nace elbash me yasa wasu masu kudin basu da adalci ne? Wanan ai rashiin sanin mutuncin Dan Adam ne, nidai tpy zanyi mayi waya, yace to shikenan.

      2 days later
Yauce ranar daya kara bamu appointment,  11am mukayi dashi ko baccin kirki banyi ba muka tafi Amma Dan renin hankali sai yace muyi hakuri Tuesday mu dawo. Min taho akan hanya mukaga mutane a tare anata hayaniya daidai jikin wani katon kamfani muka tambayi me ya faru? Sukace gubataccen ruwa ake sakar musu daga kamfanin yake Shga musu rijiyoyi da gdajensu yana illatar da Mutanen yankin sosai kuma sun yiwa shugbn kamfanin magana beyi wani Abu akai ba, shine suke zangazanga. Aikuwa nan take na fito da kayan aiki na fara dauka, sanan nayi hira da wasu daga cikin Wanda abin ya shafa. Muna komawa office na watsa, cikin kankanin lokaci gari ya dauka har gwamnati suka shiga maganar sunsa anyi magana da shugaban kamfanin kuma ya bada hakuri yace zai gyara.

Maman aysha
[9/6, 23:06] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
🔟➖1⃣5⃣

9pm
Ina kwance a daki dad ya shigo ya kwala min kira rai abace da sauri naje nace gani, me ya hadaki da alhj danladi? me kamfanin maganin sauro, OK na kwashe lbrn abun daya faru na fadamasa,   kirana yayi a waya yanata masifa wai anci masa zarafi a gdn TV na, Ashe shine marar gaskiya, is OK jeki Allah yayi miki albarka nace amin

4days later, 5:15pm
Muna kofar gdn Mr kabeer, yau shine zuwanmu na shida kenan. Muna zaune saiga PA yace bismilla mu shiga. Gidan ba karamin girma ne dashi ba, maganar kyau da tsaruwa kuwa abin baa magana saida mukaje bakin falon shiga gidan kawai saigashi ya fito da body guards dinsa oh Suleiman harka kirasu ne? Wallahi kaga wani important meeting ne ya taso min, saidai su dawo gb ya cigaba da tafiyarsa ko be ta kanmu beyi ba. Cikin bacin rai na tari gabanshi me yasa Ku masu kudi Baku da adalci be? Me yasa kuka dauki Dan Adam ba komai ba bayan kuma ko wane mutum da irin baiwar da Allah yayi masa, zuwanmu shida gidan nan bama samun ganinka wanan shi ya nuna cewa bakada cika alkawari bayan kuma cika alkawari yana daga cikin quality na salihan bayi......tasssss ya daukeni da mari ke wacece da zaki zo kina fadamin irin wanan maganar kuma har cikin gdn,  yar iska kawai, ko angayamiki ni mata suna gabana, ko kuma angayamiki ina daukar nonsense? Ku fice min daga gd karna kara ganin kafarki a gdn nan. Harya fara tafiya na kara shiga gabansa karkayi tunanin don ka mareni shikenan kaci banza wallahi bashi ka dauka, ko bayanzu ba sainayi maka abinda ya bata maka rai fiye da yanda kayimin, kuma inaso ka Sani ni ba irin yan matan da kake mu'amala dasu bace, kuma dukiyarka ko wani kyaunka baya gabana harkar aiki CE ta kawoni gdnka, kuma don kana gadara kana da kuni baka isa ka wulakanta ni ba, zan kara repeating kaina Marin da kayimin bashi ka dauka kuma wallahi saina rama. Daya daga cikin body guards dinsa ne ya iyo kaina kawai sai naga ya daga masa hanu, sanan ya kalleni cikin bacin rai yace walk out from my house juyawa nayi na kalli elbash da yayi mutuwar tsaye nace zo mu tafi. Raina a bace na shiga gd wanka kawai nayi na gabatar da sallar magriba, nayi karatun kur'ani har akayi isha'i sanan na fito falo su basma sukazo suna tayimin surutu, ni kuwa yake kawai nake sbd duk lkcn dana tuno marin da adon gari yayi min sainji kmr nayi hauka Dan bakin ciki. Dad ne ya shigo da fara'arsa Ummi na, nace naam dad gobe idan Allah yakaimu zakiyi bako, kuma koda wasa ban yadda ki wulakantashi ba nace to yayi mana sallama ya tafi

    2wks later
Naje BAGAUDA mall sayayya na fito kenan saiga jerin motocinsa sun danno kai cikin mall din tsayawa nayi INA kallonsa har aka bude masa kofa ya fito mar daga sama saiga wani mutun daga gani daya daga cikin staff din mall din ne, fada naga yanayi masa saidai bansan me yake CE masa camera ta na saita na fara daukarsa, kawai sainaga ya taskawa mutumin mari har guda biyu, bayan ya tafi na Kira mutumin muka koma gefe na tambaye shi me yayi masa yace sata yayi wa wani mutun ya bashi kaya yasa masa a mota ya boye wasu, shine mutumin yakai kararsa nace ni yar jarida ce, inaso ka juya lbrn ka da temako ka nema yayi maka shine ya mareka zanyi maka tambayoyi, idan kayi yanda nace zan baka 50k. Aikuwa ya amince

Maman aysha
[9/7, 11:39] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
1⃣5⃣➖2⃣0⃣

8:30pm
Jama'a barkanmu da warhaka, barkanmu da sake saduwa daku acikin wanan shiri namu me farin jini na ya take ne? Kamar yadda kuka Sani  ya takene? Shiri ne da yake kawo muku abubuwan alajabi, ban mamaki, da kuma barkwanci. A yau shirin namu zai fara ne da abin mamaki, abin mamakinmu nayau akan shahararran matashin me kudin nan ne kabir M Bagauda, Wanda yan mata da samari suke kira da adon gari. Wata yar iskar dariya nayi sanan naci gaba"duk Wanda ya kalli video nan dana sako muku yanzu, zaiga Mr kabeer ne ya takarkare ya taskawa wani bawan Allah mari, abin mamakin anan shine, mutane da yawa suna daukar Mr kabeer a matsayin mutumin kirki, me tausayi, kuma me son talakawa. To idan har hasashen da mutane suke masa gaske ne, me ya jawo hankalinsa ya mari mutumin da na tabbata ya haifeshi? Kuma wane irin lefi wanan bawan Allah yayi masa? Masu kallo waka a bakin me ita tafi dadi bari na hadaku da baba dattijo" baba me zaka ce game da tambayar danayi yanzu? Wato abinda ya faru shine "naji mutane suna fadin temakonsa, shine naje wajensa nima ya temaka min, Amma sai aka sami akasin hakan Ina gama fada masa matsalata kawai saiya mareni yace na tafi na bashi waje. Waw idan har zan Iya tunawa ba wanan ne karo na farko da adon gari yayi mari ba, domin kuwa ya tabayi agabana. Abin mamakin anan shine me yasa adon gari ya mari baba? Kudin da baba dattijo ya nema ne bashi da shi komai? Ko kuwa adon gari ya canja raayi daga me temakon talakawa ya koma marar temako? Naso jin amsar tambayata daga wajen adon gari saidai kash ban sami ganawa dashi ba. So masoya adon gari Ku biyomu wani satin don jin yadda zata kasance, baba dattijo ya take ne? Baba yace hakan take, wata yar iskar dariya nayi nace jama'a nima nace hakan take a madadin gdn TV na pyramid TV ni Ayshat Ahamad TURAKI nake ce muku maassalam sai mun hadu a shiri na gaba.

      Zaune yake ya kurawa TV din ido xuciyarsa band tafarfasa ba abinda da take, nan take wayoyinsa suka hau kuka friends dinsa ne suke kira Amma yaki dauka sbd yasan zancan zasu yi mishi, wani kiran ne ya kara shigowa saiyaga mum dinsa ce da sauri ya dauka hlo mum kabir me yake faruwa ne? Ya akayi a matsayinka na babban mutun a gari sukai maka wanan tozarcin? Ita yarinyar waye ubanta a gari da zatayi maka haka eye? Kodai wasu ne suka biyata tayi maka haka? Wallahi mum ni kaina banida amsar wanan tambayoyin naki, abinda na sani shine da gaske na mari tsohon, Kuma zamba cikin aminci yayi, kuma kinsan ba mutumin dana tsana a duniya irin me cin amana, shi yasa na mareshi. Amma karki damu mum insha Allah zan dsuki mataki akai. Mikewa yayi ya kalli Sulaiman da jajayen idanuwansa tunda uwata ta haifeni baa taba bata min rai irin Wanda yarinyar nan tayimin ba, wallahi saita raina kanta, kuma saita gane dukiya ba karya bace, duk Wanda yake da kodi yafi karfin wulakanci. Ka fadawa Barr Bashir gobe inason mgn dashi, to shikenan ranka yallabai saida safe.

    Zuciyata tayi fari tas don na tabbata duk inda adon gari yake yanzu yana nan acikin bacin rai, wayata na dauko na kira baba dattijo nace baba kana ina? Yayi min kwatancen inda yake nace to ka jirani INA zuwa yanzu. Baba abinda nakeso dakai shine ka tattara kayanka kabar garin nan sbd zaka Iya shiga matsala, a wane gari kake? Yace Adamawa, OK to zan kara maka yawan kudin ya zama 150k don Allah baba ka tsarkake zuciyarka kaje kaja jari dasu, kaji tsoron Allah, kayi Sana'a ka nemi na kanka. To nagode Allah ya zaka miki da alkairi, dama talauci ne yasani, Amma insha Allah zanje naci gaba da sanaata ta saida gwanjo. Saida na saukeshi a tasha ya shiga mota sanan na tafi gida cike da farin ciki

Maman Aysha
[9/7, 15:32] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
2⃣0⃣➖2⃣5⃣

Wacece Aisha Ahamad Turaki?

Yace ga Alhj Ahamd TURAKI, Dan kwangila Wanda yayi suna duk area Kano ba Wanda be San da zamansa ba, haifaffan garin bichi ne, kuma hamshakin me kudi ne daya mallaki kamfanoni da gidaje, kuma shine mamallakin gdn TV na pyramid TV. Matanshi biyu ne, Haj bilkisu itace uwr gd yayan ta biyu Zainab da samira, ita kuma amaryar sunanta Haj Jidda yayan ta uku aysha ce babba saida aka haifeta da shekara goma sanan aka haifi yan biyu wato basma da Ahamad, alhaj sbd tsananin murna yasawa Ahamad sunansa shine ake kiransa da junior. Alhaji yana tsananin son amaryarsa sbd tanada kirki gata da son addini. Idan yana tare da ita mantawa yake yanada wata matar, kuma yanda yake tsananin sonta haka yake son yayanta, duk Wanda ya shiga gdn alhaj Ahamad a kankanin lkc zai gane alhaji yafi son Haj Jidda da yayan ta. Gabady yayan nasa sunyi degree idan ka dauke yan biyu. Zainab political science ta karnta, public admin  ita kuma aysha mass communication. Da Haj bilkisu da yayanta a bichi suke da zama, ita kuma Haj Jidda a Kano da alhaj ya gama ginin damfareren gdnsa saiya debosu ya hadasu waje daya Amma kowa da part dinsa. A yanzu haka Zainab shekararta 24, samira 22 aysha kuma 18yrs.

Waye kabeer M Baugauda?
Dane ga marigayi senator muhd Tahir BAGAUDA, mahaifinsa mutumin kirki ne kuma adali Dan asalin BAGAUDA ne shekararsa 12 yanayin senator a Kano, ya kawo cigaba a jahar Wanda tunda suke samun Dan siyasa baa taba samun me kirki da temakonsa ba, wanan shine dalilin da yasa sukai ta zabarshi har saida yace ya gaji, ba a siyasa kawai ya tsaya ba idan akazo harkar business ma shahararran Dan kasuwa ne ya mallaki kamfanoni da yawansu zai kai 40, banda sauran kadorori. Matarsa daya Haj asma'u da yayanta biyu wato Salma itace babba barrister ce, tana auran wani house reps a abuja take da zama, sai kaninta kabeer shi kuma civil engineer ne he very handsome, so kind, intelligent and very respectful. Mahaifinsu ya rasu ne a  hatsarin mota akan haryarsa daga abj zuwa Kano, ba Iya iyalansa ne sukayi rashin sa ba, gabadaya Mutanen 9ja ne sbd alhaji mohd dattijon arziki ne. Bayan an raba gado sai kabeer yaci gaba da kula musu da dukiyar, kuma yana samun kwangila sosai sbd governor me ci a yanzu aminin babansa ne, babansa ne ya fara sashi a siyasa, kuma ba lefi ya rike alkawari sosai. Tun rasuwar mahaifinsa ya maye gurbinsa wajen temako da kaunar talakawa, har yaso yafi mahaifinsa ma, mata basa gabanshi kuma bayasan reni. Mutane ba karamin mamaki sukayi ba da sukaga program ya take ne? Da aysha ta nuna sbd kowa yasan ba halinsa bane

Cigaban labari

Maman aysha
[9/8, 09:50] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
2⃣5⃣➖3⃣0⃣

Cigaban labari

Daga tashar gd na wuce naje nayi wanka nayi sallah, sanan na fito falo ina cin abinci muna hira da mum, su basma kuma sun Dora Kansu akan cinyata. Abba ne ya shigo yayi dariya kaga mummyn yara me kuke tattaunawa ne da yaran naki? Murmushi mum tayi sanan tace hirar duniya muke, mikewa nayi zan koma naki don naga alama yau dad acikin soyayya yake😀, kawai sainaji yace zauna ummina magna nake so muyi dake, kinsan alhaji Lawan mati? Eh Abba, deputy governor ko? Yawwa yar gari, tare muke dashi yanzu haka yana guest Palo, shine bakon danace zakiyi last WK kuma be sami damar zuwa ba sai yau, inaso kiyi sauri ki shirya kije karki bata masa lkc, sauran bayani idan kin dawo kyaji. Jiki ba kwari na tashi na koma daki, dama gown ce ajikina rolling kawai nayi na fita. Har kasa na durkusa na gaishe shi sanan ya kalli securities dinsa yace Ku bamu GU, da rawar jiki suka fice sanan ya dawo da hanklnsa wajena ba saina yi introducing kaina ba, nasan kinsan koni waye. Ina daya daga cikin masoya kallon program din da kike na Ya Take Ne? Kullum bana missing dinsa, idan ina kallo har wani nishadi nake,da ina ganin kamar program din ne yake birgeni daga karshe saina gane ke nakeso, na kamu da sonki alokacin da bansan lokacn daya shiga ba, ina tsananin sonki Aysha, kuma bazan boye miki ba matana biyu da Yaya goma. Ya salam haba baba don Allah, sona fa kace kanayi? Ba Kaine Baban su nazifi Lawan ba? Yes nazifi Dana ne, Amma kuma kace kanason karamar yarinya kamar ni, iam just 18yrs fa, don Allah ka rifamin asiri ka janye wanan maganar pliss. Bazan Iya ba Aysha da zan Iya janyewa da ban tari mahaifinki da mgnr ba, nayi kokari naga nayi ignoring abin Amma na kasa, don Allah ki temaka min aysha wallahi ina tsananin sonki, yanzu zan baki lkc kije kiyi tunani akai, zan dawo jibi in Allah ya kaimu na barki lpy. Jiki ba kwari na shiga Palo su mum suna nan zaune yanda na barsu dad ne ya kalleni harya tafi? Nace eh, to zo ki zauna nace to, sanan ya fara magana "alhaji Lawan uban gidana ne, yayi min abubuwa na alkairi Wanda bazan Iya saka mishi ba saidai nayi masa addua kawai. Tunda name dashi ban taba Neman Abu a wajensa na rasa ba, kullum addua nake Allah ya kawo ranar da zai nemi wani Abu a wajena, nima na saka mishi da abinda yake min, kwatsam sai gashi yazomin da maganar yanaso na bashi auranki. kuma aduniya ba abinda alhaji Lawan zai nema a wajena banyi mishi ba, sbd haka inaso kisa aranki shi na zaba miki a matsayin miji, kuma nasa date din daurin aure nan da 2 wks. Sanan lawyer n Mr kabeer yazo ya sameni yace mu tabbatar mun wanke Mr kabeer akan kazafin da akayi masa idan ba haka zasu shigar damu kotu,kuma kinsan banida kudin da zan Iya ja dashi, sbd haka inaso ki wanke shi a shirinku na gobe da zakiyi. Mum ce tace Amma daddyn yara taya zaayi ka rasa Wanda zaka aura mata sai tsoho, mutumin daya fika a hafe ma. Ya isa ya dakawa mum tsawa (abinda be taba mata a gabanmuba) indai akan alhaji Lawan ne karki kara yimin magana, na Riga na gama yanke hukunci, Ya mike ya tafi daki. kuka nake me taba zuciya mum me yake shirin faruwa dani ne? Me yasa dad ya zabi farin cikin uban gidansa fiye da farin cikin yarsa daya Haifa? Wallahi mum bana sansa tsohone sosai don Allah kiyi wani Abu akai. Kiyi hakuri Aysha zan yi mishi magana insha Allah bazaki aureshi ba, muje ki kwanta bazan taba barin farin cikin ki ya rushe ba, saida ta rakani har daki na kwanta sanan ta tafi, murmushin jin dadi nayi nace mum ba karamin sona take ba Allah ya bamu ikon yimusu biyayya.

     Mama ce zaune a tsakiyar yayanta inajinki samira kikace deputy governor ne yazo gdn nan eh wallahi mama wata yar iskar dariya tayi lkc yayi da zan tarwatsa rayuwar Haj Jidda, na tabbata bazata so yatta ta auri tsoho ba kunga akwai rigima kenan, sabd haka zanje na sami boka dankundalo yayi min aikin da zasuyi rigimar da zata zama sanadiyar barinta gdn.

Maman Aysha
[9/9, 11:33] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
3⃣0⃣➖3⃣5⃣

Banyi wani baccin kirki ba inayin sallar asuba na zauna kart har saida rana ta fito, nayi addua na roki Allah ya fitar dani daga halin da nake ciki. Jiki ba kwari na tafi na hada break past, sanan nayi wanka, na tashi twins din mum ma na musu sukaci abinci sanan na kaisu sch. Gida na dawo na kwanta banda tunani ba abinda nake dad ya rasa Wanda zai auramin sai tsoho? Yaushe dad ya zarme da son kudi da har yake son kuntata rayuwa ta? Why dad don Allah kuka me karfi yaci karfina, saida nayi me isata sanan naje na wanke fuskata. Sai wajen 10 suka tashi ina jin motsinsu na fice naje na durkusa na gaishe su dad yace ummina lpy baki fita aiki ba yau? Murmushin karfin hali nayi nace yanzu zan fita, yau bamu da aiki da yawa ne shi yasa. Alright, ya zauna yayi break sanan ya fice. Mum ce ta kalleni ana ganin fiskarki ansan kinyi kuka Aysha, don Allah kiyi hakuri ki fitar da mgnr nan a zuciyar ki, insha Allah komai zai daidaita kinji dota na nace Allah yasa mum tace amin, ke kinci abincin ne? Nace aa, to zauna kici. Sai wajen 11am na shiga office, ina shiga elbash ya biyo bayana beauty meke faruwa ne yau? Na kiraki yakai sau goma bakiyi picking ba, dama wani mutun ne ya kawo kukanshi, wai wani alhaji yasa anyi nakiya irin wacece ake idan zaa fasa dutse a jikin gdnsa, as a result ginin yana Neman rushewa, kuma ya fadawa alhajin Amma yaki ya tausaya mishi, so shine nakeso muje mu dauko gdn, abi mishi hakkinsa, nace to muje. Beauty yau kalau kk kuwa? Duk da nasan you're calm, Amma yau shirun naki yayi yawa, is like akwai abinda yake damtafi? Ba abinda yake damuna muje kawai, ban yadda ba don Allah ki fada min, ya salam elbash banason mgn da yawa fa, dariya yayi yace oh I see ashefa yan jarida basa son mgna, nima dariya nayi muka fita a tare.

         8:pm
Jama'a assalamu alaikum barkanmu da sake saduwa acikin wanan shiri namu na Ya Take Ne? A yau shirin namu zai fara ne da bawa the youngest multi billionaire Mr kabeer wato adon gari hakuri akan akasin da aka samu a shirin mu daya gabata. Kamar yadda kuka Sani pyramid TV gdn television ne da yake yada abubuwa domin a kwatawa talakawa yancinsu, wanan shine dalilin da yasa muka haskawa jama'a abinda baba dattijo ya sanar mana saidai da muka tsananta bincike mungano cewa abinda ya fada mana ba gaskiya bane sbd haka don Allah pyramid TV na Neman afuwa a wajen adon gari da masoyansa. Shirin da muke tafe dashi acikin wanan sati shine.......
                  Jama'a anan muka kawo karshen shirin mu na wanan satin, ina me matukar godiya ga masoyana, kuma ina me bakin cikin sanarda masoyana cewa daga yau bazaku kara ganina ba, idan da Wanda na taba batawa rai daga lkcn Dana fara gabatar da wanan shiri zuwa yanzu don Allah su yafemin, amadadin hukumar gdn pyramid TV ni ayshat Ahamad TURAKI nake cewa bissalam.
          Ina fita daga show room din office dina na shiga na kifa kaina a table ina kuka me taba zuciya shikenan rayuwata ta ruguje wanan wane irin kaddara ne kuka nake sosai. Elbash ne ya shigo office din aidama na fada yau ranki a bace yake kk musamin, kuma naji kin fadawa mutane cewa daga yau bazasu kara ganin ki ba, akwai abinda kk boye min beauty, don Allah ki fadamin me yake faruwa dake? Ko duk shakuwar da mukayi har yanzu bankai matsayin da zaki fadamin damuwarki ba? Ba haka bane elbash, to indai ba haka bane fadamin what is wrong with you? Auran dole dad yakeso yayimin da mutumin da ya girmeshi ma ahaife, wai deputy governor dad yake son aura min nan da 1 wk, kukane yaci karfina don Allah kababi shawara elbash yanzu ya zanyi? Kiyi hakuri kiyi biyyaya Aysha, kana nufin nayi biyayya na auri tsoho me mata biyu da yayya goma? Na Sani is unfortunate Aysha, Amma idan kk mishi biyayya Allah sai yayi miki zsbin abinda yafi alkairi. Shikenan zan duba na gani, ni zan tafi saida safe to Allah ya kaimu

Maman Aysha
[9/9, 21:58] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
3⃣5⃣➖4⃣0⃣

Washe gari
Yau ko office na kasa fita haka na wuni jiki asanyaye saidai INA kokari boye rashin hankalin da nake ciki sbd kar mum ta damu.

    5pm
Zuciyata tace take min zafi, abin duniya ya dameni kuka kawai nake sonyi gashi ba dama mun tana nan, kawai saina yanke hukuncin fita zaga gari ko naji sanyi a zuciyata. Shiryawa nayi cikin wata English gown yellow rigar ta hadu sosai wajen 25k aka sayeta nayi rolling da wani karamin yellow mayafi sanan NASA black shoe&bag na manna dark brown glass nayi kyau sosai, sanan na shirya su basma da junior muka fito nacewa mum zamu Dan fita zaga gari tace to sai kun dawo Amma karku Dade kinsa yau Excellency zai zo nace to, na kama hanunsu muka nufi motata. Direct rose flower sweet and bakery muka tafi, wani waje ne dayake tashe akano adon gari ne ya bude wajen, sbd shima time to time yana zuwa ya huta awajen, Amma fa wajen yayyan masu kudi ne domin kuwa idan kudin ka bekai 20k ba, baka isa ka shiga wajen ba. Wajen a zagaye yake da lafiyayyun flowers kala kala, shi yasa akasa masa suna rose flower sweet and bakery. Wajene daya tattara haddadun yan mata da samari, Amma fa yayyan masu kudi, kuma dama don yan mata da samari kawai adon gari ya bude wajen. Muna shiga naje nayi mana ordering ice cream, pizza da kuma shawarma wata kujera na samu muka zauna na budewa su junior ice cream din na basu suna sha suna wasan su. Shiru nayi inata kallon yan mata da samarinsu kowa yana harkar gabansa cikin farin ciki da annushuwa, Abin very interest, nan take na tuna irin mijin da zan aura tsoho me yayya goma, ina!! Bazai yiyyu ba wallahi ai idan kanaso ka mure rayuwar aure to ka auri yaro daidai dakai, Amma tsoho me zai Iya? Wasu zafafan hawaye ne suka fara yawo a kumatuna, kamar daga sama sainaji wasu yan mata sun hada baki wajen cewa waww!! ADON GARI, Kuma a lkc guda naga gabadaya hankalin yan matan wajen yayi gunsa harda wadanda suke tare da samarinsu, nima juyawa nayi domin na kashe kwarkwatar idona. Sanye yake cikin wasu shegun black jeans and shirt, a jikin shirt din an rubuta SMART GUY da red paint, sanan ya Dora red jacket akai gashin kansa ya kwanta yayi lub gwanin ban sha'awa, yasa red flat cover shoe me mugun tsada, idonsa a rufe yake da Dan karamin farin sun glass dauke yake da murmushi a  fuskarsa da alama waya yake, kuma daga gani wacece yake wayar da ita tana da matukar muhimanci awajensa. Haka yazo ya wuce ta gabanmu da body guards dinsa guda 6 ya nufi wani special waje  da akayi fencing da wasu shegun flowers kuma aka zuba lafiyayyun kujeru na hutawa aciki.dama sbd shi aka tanadi wajen. Daya daga cikin yan matan da suke gefena tace alhamdulilla yau kwana na biyar ina zuwa wajen nan sabd naga adon gari Amma ban ganshi ba sai yau, dayar tace ni kuma zuwa na uku kenan, dayar da aka kira da Rashida tace oh iska tana wahalar da me kayan kara Ku duba fa kuga duk kafe shi da idon da mukayi muna kallonsa shi besam ma munayi ba. Nima a zuciyata nace tabbas adon gari ya hadu ba karya, lkcn da mukayi fada dashi ganin tsoro nayi masa shi yasa ban kare masa kallo ba, inama yace yana sona, nan take na tuno da matsalar da take gabana ta auran tsoho bansan lkcn dana fara kuka ba, kifa kaina nayi akan table inata gurzar kuka.
        Basma da junior kuwa suna ganin wucewar KB sai suka bi bayansa har cikin wajen suka farayi masa surutu, yaran sun burgeshi sosai besan lkcn daya beye musu ba sunata bashi dariya yace wa yazo daku nan sukace da auntynmu muka zo, yace OK, apple ya dauko ya basu sukai ta murna. Saida nayi kuka me isata harna gaji, na manta nazo da yara saida na duba inda suke wasa naga ban gansu ba, nan take na fara nemansu duk inda nake tunanin zasu na duba bangansu ba saida naje har bakin gate din shigowa Amma ba alamsrsu. A bangaren yaran kuma, KB zai tafi sai ya kamo hannunsu yace muje na rakaku wajen Aunty nku ni zan tafi gida, da suka nuna mishi inda na zauna sukaga bana nan ran KB ya baci kallon su yayi yace tuda auntynku ta gudu ta barku muje na kaiku gdna shikenan na sami yayya, zaku Bini sukace eh a tare, aikuwa yayi wajen motarsa dasu. Ni kuma a dawo daga bakin gate kenan cikin fargaba da tashin hankali kawai sainagano su suna shirin shiga motar, da sauri na tafi wajen Malam ya haka? Kawai daga ganin yara saika sasu a mota, Ashe suna wajenka, inata shan wahalar nemansu........Shut up marar tarbiya kawai, kin tafi yawon banza kin barsu, wa ya fada miki ana zuwa da yara nan wajen? Inaso ki Sani daga yau idan zaki fito yawon iskancin ki karki kara tahowa dasu, ki barsu agida. Kallonsa nayi da idona daya gama rinewa sanan nace ni ba yar iska bace, kuma idan har nasan yawon iskanci zanzo ai bazan tahoda yara ba, kuma idan da gaske iskanci ake awajen nan ai kafi kowa daukar zunubi tunda Kai ka bude wajen, nagode da kulawarka akan kannena. Wani irin kallo tsana ya bini dashi sanan yace stupid girl. Ban kara bi ta kansa ba na kama hannunsu muka tafi.

Maman Aysha
[9/10, 12:11] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
4⃣0⃣➖4⃣5⃣

8:15pm
Na idar da sallar isha'i ina zaune ina lazimi na jiyo muryar dad yana kwalla min kira da sauri na fita, ina zuwa yace kiyi masa ki shirya Excellency yana jiranki cikin fargaba nace to, haka kawai naji gabana yana faduwa. Dake ban cire hijabin da nayi salla ba takalmina kawai nasa na fice. Saida nayi addua sanan nayi sallam na shiga ya amsa yana bina da wani mayyatacen kallo. Dukusawa nayi na gaisheshi, sanan yace kamar yadda mahaifinki ya Sanar dani kun riga kun gama magna, so bana bukatar jin ra'ayinki akaina. Abinda ya kawoni shine inaso kiyi list din abubuwan da kk bukata na hidimar biki. Cikin tashin hankali na dago muka hada ido dashi kawai saina fashe da kuka lalle ka tabbata marar adalci, sbd da kana da adalci danka yakamata ka nemawa aurena bakaida kanka ba, kuma kai mutun ne me tsananin sonkai sbd baka damu da yanda rayuwata zata Kasan ce ba idan na auri tsoho irin ka, kai kawai burinka ka mallake ni, to wallahi inaso kasani bana sonka, bana kaunarka, kuma wallahi saidai akai gawata gdnka domin kuwa dana aureka gara na kashe kaina da gudu na fice na barshi a wajen ina kuka me tsanani, mum tana zaune a falo(dake yau dad a part din mama yake) na wuceta da gudu na shiga dakina, cikin tashin hankalin ta biyoni me ya faru Dota? Me yasameki kk wanan kukan haka? Mum wallahi bana son shi, wallahi idan na aureshi mutuwa zanyi. Zatayi mgana kenan naga ambanko kofar dakin da sauri dad ne cikin bacin ran da bantaba gani a fuskarsa ba yace Ku fito falo inason ganin ku . mum ta kama hannuna muka fita, muna zuwa muka sami mama da Zainab da samira a zaune, cikin kakkausar murya dad ya fara magna Aysha naji rashin kunyar da kikayiwa Excellency, kin nunawa duniya cewa ni ban isa dake ba. Tabbas bahaushe yayi gaskiya da yace tsintacciyar mage, bata mage, wanan Karin magana haka yake. Yau zan fada muku abinda Baku taba Sani ba, kawai sainaga mum ta mike a zabure ta durkusa ta rike kafafunsa tana wani irin kuka me tsanani don Allah alhaji kayi hakuri da fadar maganar nan, kayimin alkawari ba Wanda zaiji mgnar nan meyasa zaka fada yanzu? Wata mahaukaciyar tsawa ya daka mata yimin shiru ko ban fada yanzu ba dama wataran dole maganar ta fito, cikin wata dakkyakiyar murya yace Aisha nace na'am inaso yau ki Sani bani na haifeki ba.....innalillahi was inna ilaihir rajuun juyawa nayi na kalli mum nace waye mahaifina? Kamar daga sama naji muryar dad yace itama ba ita ta haifeki ba nan take na fadi sumammiya da gudu aka sami ruwa aka yayyafamin sanan na farfado rungume mum nayi ina kuka me  tsuma zuciya nace mum don Allah kice min ba gaskiya bane, don Allah kice ba gaskiya dad yake fada ba, batayi magana ba sai kuka da take me tsanani. Mutsitsika idona na farayi ya Allah kasa mafarki nake....muryar dad ce ta katseni da cewa ba mafarki kike ba dagaske ne bamu muka haifeki ba, wato abinda ya faru shine....

      18yrs back
Nakai Jidda asibiti bada shirin haihuwa mukaje ba sbd cikin wata 7 ne, saidai muna zuwa da aka dubata sai akace haihuwa ce, haka na zauna inata addua har Allah ya sauketa lpy, da sauri nurse din tazo tace na kawo kayan baby, sai alokacun na tuna bamu dakko ba, sai nace Amma zanje na kawo yanzu tunda ba nisa sosai. Harna shiga mota zan tayar sai nurse din ta kara fitowa da sauri tacemin iam sorry to say babyn ta koma, saida ka debowa uwar kayanta jiki ba kwari nace to na tafi. Na wuce ta jkin wani gdn gona saina hango cincirindon mutane, sai nima na karasa wajen na tambayi me ya faru sukace wata mata ce ta sato jaririya, ta fada cewa wani Dan siyasa ne yasata ta sato masa yar, Amma bata karasa bayani ba ta mutun, nace INA yar aka miko min ke kinata shan hannu kina kuka, shine na roki yansanda da su barmin ke zan rikeki. Nan take mukaje police station aka bude miki file, suka bani takardu nayi signing aka kafa shedu, sanan na basu cikkaken address dina, na barki a hannun yan sandan na koma asibiti  bayan ansallamo Jidda direct police station muka wuce, nayi mata bayanin komai sanan na damka amanarki a wajenta tare da alkawarin ba Wanda zaiji sai ranar auranki.

         Wanan shine abinda ya faru kuma nayiwa Excellency bayanin komai yace ya yadda zai aureki a haka, Amma dake baki da mutunci, kuma ke ba gudar jinina bace kika ki bin umarni na, sbd haka inaso ki Sani daga yau bani bake, ki tattara komatsanki kibarmin gdna sbd ko yar Dana Haifa acikina bata isa ta kaucewa umarnina kuma naci gaba da zama da itaba, ballantana ke yar tsintuwa, sbd haka ki manta da kin taba sanin wani me kama dani arayuwarki, mun rabu dake har abada. Mum yace idan ka mata haka bakayi adalci ba, ina kake tunanin zata nufa yanzu? Ta tafi ko inama niba damuwata bace. Tabbas ba damuwarka bace sabda bakai ka haifeta ba, Amma inaso kasani ba ita kadai ka kora ba harni ka kora domin kuwa bazan taba zama agdn nan ba tare da Aysha ba.

Maman Aysha
[9/10, 15:15] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
4⃣5⃣➖5⃣0⃣

Mama ce tayi wata shewa aidama ance sannu sannu bata had a zuwa, nidama nasan komai Daren dadewa asiri zai tonu, an Dade ana nunawa yayyana banbaci agdnan akan ki Ashe ma yar cin arziki ce, Allah ya raka taki gona. Haka na mike na fara Jan kafata da kyar na shiga daki da tattara kayan da nasan zasu min amfani, na janyo katuwar troly na hayen idona ya kafe, Ashe idan mutun yana kuka da hawaye ma rahamane? Falon na dawo na durkusa agaban Abba nace ga mukullin motarka nagode da kulawar da kuka bani, kuma harna mutu bazan taba taba mantawa da abinda kukayimin na alkairi, nagode Allah ya saka muku da alkairi Allah ya biyaku da gdn aljanna. A dakire yace ki rike motar ai taki ce, jiki ba kwari na mike nace mum don Allah ki yafemin, nasan kinyi dawainiya dani irin wadda kowacce Uwa takewa danta,kinyi fama dani tun ina jaririya nagode Allah ya saka miki da mafificin alkairi, kuma insha Allah zanci gaba dayi miki addua irinta da da mahaifi harna koma ga mahallicina, nagode Allah ya kaddara saduwarmu. Jan trolley nayi nafara tfy, da sauri mum ta rike hannuna jirani nazo mu tafi Aysha, ai nima na gama zama a gdnan sbd yau alhaji ya tabbatar min da ya daina sona, tunda ya koreki banga amfanin cigaba da zama dashi ba, alhaji rubutamin takarda ta mu taffadAi idan kinga mun rabu saidai idan mutuwace ta raba, kuma in banda ke da abinki kin manta cewa ni na baki amanar Aisha, kuma yanzu na karba sbd haka yanda na koreta kema dole kiyi hakuri da ita barima ki gani, wayarsa ya dauko ya kira abbanta bayan sun gaisa ya fada masa duk abinda ya faru, shi kuma yace a bata wayar yana bata abbanta yace mijinki ya fadamin abinda yake faruwa, sbd haka kibi umarnin sa idan kika sake kika fita daga gdn bada izninsa ba, ban yafe miki ba kina jina ko? Cikin tsananin kuka tace eh, sanan dad ya kalleni yace you can go. Harna je bakin kofa mum ta kara kirana daki ta koma ta debo wasu kaya ta miko min, wanan sune kayan da suke jikinki lkcn da muka karfeki, wanan kuma zanin goyen ne, wanan kuma sarka tace lkcn dana saya 500k ce Amma yanzu nasan tafi haka ki sayar kiyi amfani da kudin. Inayi miki addua Allah ya takaita miki wahala, yayi gaggawar hadaki da iyayenki cikin dauko, Allah yayi miki albarka kawai ta juya daki da sauri, nima da gudu na bude motata na fita daga gdn.

     AmmaTafiya nake Amma bansan inda na nufa ba, saida nayi tafiya me nisa har na Dan wuce BUK new side sanan na tsaya a gefen titi na kifa kaina akan sitayari na fara kuka, ban farga ba naga 10:45pm na kalli wajen da nake ko motsin mutane babu, elbash ne ya fadomin a rai kawai saina kirashi hlo beauty ya akayi? Kazo kan titin gwarzo road gaba da new side kadan ina wajen. Tuki yake kamar zai tashi sama sbd shi a bompai yake, akwai nisa a tsakaninsu Amma sabd gudun da yake sharawa, kuma ba yawan motoci sbd dare ya fara a 30minute yaje wajen acikin mota ya sameni beauty meya faru kika zo bayan gari kika zauna? Cikin kuka nace komai ma ya faru elbash su dad basu suka haifeni ba, bansan iyayena ba, ba wani mutun da zan nuna nace Dan Uwana ne, bansani ba ko iyayena suna dare ko babu dad ya koreni a gdnsa yanzu banida kowa aduniya kuka yaci karfina. Ya salam Aysha zaki Iya driving? nace eh, to shiga mubar wajen nan ki shiga gaba zan ringa binki a baya zoo road zamu kinji nace to.

Maman Aysha
[9/15, 11:22] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
5⃣0⃣➖5⃣5⃣

Tun a hanya ya sanar da Yaya bilal suna zuwa brodan Elbash ne Uwa daya uba daya. suna isa kofar gdn aka bude musu gate suka shiga da motocinsu matar Yaya bilal da faraarta ta karbe mu, sanan aka kaimin kayana guest room, elbash ya kira yayanshi gefe yayi masa bayanin komai sanan ya rokeshi alfarmar na zauna a gdnsa zuwa next WK idan amaryarsa ta tare sai na koma gdnsa. Ni kuwa tunda na shiga guest room din nake kuka Wanan wane irin rayuwa ce? Dad meyasa kayimin haka don Allah? Me yasa bakayi hakuri kaci gaba da zama dani ba why pliss? Kuka nake me tsanani kaina banda ciwo ba abinda yake elbash ne ya shigo dakin Aysha har yanzu baki dena kuka ba? Don Allah kiyi hakuri nasan kina cikin wani hali Amma ki sani akwai Allah, kuma shi yafi kowa sanin abinda yasa kika sami kanki acikin wanan halin, inaso ki mika al amuranki a wajen Allah, kuma kiyi tawwakali insha Allah zai zame miki alkairi, nima nabar aiki a pyramidTV, sbd ke dama na nemi aiki a wajen, so tunda yanzu bakyanan nima dole na tafi. Wato abinda ya faru kafin na fara aiki a pyramid TV ina daya daga cikin masoya kallon program dinki, kuma cikin lkc kadan naji na kamu da sonki kawai saina yiwa dad dina mgn inaso ya Samar min aiki a pyramid da yaki Amma dana matsa masa dole yaje ya sama min, ranar dana fara reporting na roki manaja daya hadani aiki dake sbd na sami saukin samun kanki, saidai Dan banzan kwarjininki ya hana nayi miki mgn, daga baya saina gane kinfi karfina sbd ke zubin matar manya ce irinsu adon gari, tun daga lkcn na canja son da nake miki da irin Wanda Yaya yakewa kawarsa, ina tsananin sonki beauty ina jinki tamkar ciki daya muka fito dake. Sbd haka don Allah ki dena cewa baki da kowa ni zan zame miki Uwa, uba, kuma broda in Allah ya yadda zan rikeki a bisa amana kuma zan temaka miki wajen nemo familynki. Na sami aiki a CBN kuma next WK ne daurin aurena Sbd haka zaki zauna anan gdn zuwa next WK idan amaryata ta tare saiki koma gdn, kuma munyi shawara da Yaya zan yiwa daddynmu mgn ya Samar miki aiki, Sbd kwanan zaa Debi maaikata, kuma dad dinmu ne chairman na civil service commission. Don Allah kiyi hakuri ki cinye jarabawar da Allah ya Dora miki kinji beauty nace to fita yayi ya kawomin yoghurt da pcm nasha sanan na kwanta ya rufemin kofar ya tafi.
[9/15, 15:40] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
5⃣5⃣➖6⃣0⃣

Haka naci gaba da rayuwa a gdn Yaya bilal, matarsa aunty Kulsum tanada kirki saidai na fahimce dana da kishi sosai, shiyasa nake kaffa kaffa saina tabbatar mijinta ya fita office sanan nake fitowa na tayata aiki, sanan yana dawowa nake komawa daki bazan fito ba sai baya gdn. Kullum elbash ya zuwa musha hira dashi yana Iya kokarinsa yaga ya Sani walwala da farin ciki, gabadaya lkcnsa ni yake bawa shi kullum burinsa ya ganni acikin walwala, yauma as usual elbash yazo muna ta hira sai aunty Kulsum tace gaskiya ina tausayin amaryarka elbash, me yasa kikace haka aunty na? Gani nayi kullum anan kake yini, ko irin Dan shirin nan da angwaye suke kai bakayi, dariya yayi yace su sadik abokina sun gama shirya komai, shiyasa na taho wajen yar kanwata ko beauty? Murmushin yake kawai nayi.

        1 WK later
Yaune aka fara gudanar da bikin elbash, run da aka fara bikin ko waya elbash baya samun damar kira, aunty Kulsum ta bukaci da muje wajen bikin Amma naki sabd nasan staff din pyramid TV zasu, koma duk jama'a sun San abinda ya sameni, so banaso na hadu dasu, ba kunya tace min ni kuma banaso na tafi na barki da mijina a gd, Sbd gaskiya kinada fitinennan kyau idan na barku komai zai Iya faruwa shiyasa nake tsananin tausayawa amaryar elbash Sbd zata kunshi bakin ciki. Yanzu kiyi tunanin inda zaki ki zauna kafin na dawo, wasu zafafan hawaye ne suka zubomin nace bari naje gdn siyama kawata, idan kin dawo saikimin waya, to shikenan, ni na fara fita daga gdn sanan ta tafi gdn surunkanta inda ake gudanar da bikin

1wk later
Anyi biki angama lpy amarya ta tare a gdnsa dake ring road dad dinsa ne ya Gina masa gdn kyauta ya bashi. Ina daki a kwance ina aikin kuka naji muryarsa aunty Kulsum tana tsokanarsa ango kasha kamshi sai yau aka sami damar fitowa, haka dai suka gaisa ya shigo dakina ya salam beauty har yanzu baki dena kuka ba dauki mayafiki mu tafi shi ya dauki trolley din muka fito nayiwa aunty kulsum godiya muka tafi.  boys qtrs din gdnsa ya bani ciki da falo da toilet ne gdn nasa yayi kayau sosai sabd zaikai 15 million shi kanshi ginin BQ din yayi kyau, kuma elbash ya gyara min duk wani Abu najin dadin rayuwa ya sakamin Sbd TV plasma me kyau ya saka. Bayan mun ajiye kayan yace akwai abinda kk bukata ko abinda be miki ba? Nace komai yayi nagode allah ya saka maka da gdn aljanna yayi murmushi yace amin, sanan yace  mu shiga ciki yayi introducing dina awajen amarya tunda muka shiga naji gabana yana faduwa  kujera ya nunamin yace na zauna ya kira ta nace to. Sun dade kafin su fito, harna fitar darai dasu sai gasu ta makale ajikinsa kaina yana sunkuye har suka karaso suka zauna ina dago  kai muna hada ido naga ta mike cikin bscin rai tace Aysha Ahamad TURAKI itace yarinyar dakake fada cafdi ai wallahi bazai yiyyu ba gaskiya ban yadda ba idan sonta kake kawai ka aureta Amma ya zaayi na zauna da wanan kyakyawar yarinyar agida daya bayan ba muharramarka bace shut up Rahama ban kawo Aisha gdn nan ba saida kika amince, me yasa yanzu zakimin haka? Da zan aureta da ban aureki ba sabd na riga saninta kafin ke, na dauki Aysha ne tamkar blood sister na kuma bazan miki dole ba, idan har kince bazaki zauna da ita ba bazan takura miki ba ke matata ce kuma ina sonki so kinga Dole na baki hakkinki, Amma inaso kisani zuciyata bazata taba yafe miki ba domin kuwa kin hanani na aikata aiki na alkairi. Cikin kissa tace ba komai angona magna ta wuce na hakura Allah yasa haka shi yafi alkairi cikin farin ciki yace amin nagode, sanan yace don Allah inaso ki riketa a bisa amana kinga kin girme mata shekararki 22, ita kuma 18 so kinga a matsayin kanwa take a wajen ki Sbd haka don Allah ki rike amana saida tayi wani fari da ido sanan tace ba matsala sanan ya kalleni yace Aysha ki dauki rahama a matsayin yayarki kinji nace to zama tayi akan cinyarsa swit heart na hada maka zobon fa na dauko maka? Ina ganin haka na mike nace zan koma daki saida safe elbash yace tsaya kisha zobo mana nace na gode, na fita na koma daki saida nayi kuka me isata sanan nayi bacci. Washe gari bayan elbash ya fita wajen aiki aunty rahama tazo ta kirani nayi mata aiki haka na wuni ina aiki har girki ni nayi mata tana kwance. Haka rayuwata taci gaba agdn kullum wuni nake ina aiki saita dadaici ya kusa dawowa sanan tace na koma part dina aunty Kulsum matar Yaya bilal ta kara zugata tsana take nunamin a fili kwata kwata banajin dadin gdn, gashi elbash idan ya fita tun 7am sai 6pm yake dawowa. Gashi ta hana shi zuwa part dina, sbd tace idan ya kara shiga saita fadawa iyayensa ya kawo mata karuwa ya ajiye a gd, shiyasa yake lallaba ta yanzu mostly saidai muyi mgn dashi a waya, Amma duk da haka yana Iya kokarinsa yaga ya kyautata min.

       2wks later
Elbash ya shigo da farin ciki yace albishirnki nace goro yace an daukeki aiki zaki ringa koyarwa a wata secondary sch a yankaba da murna na karbi offer nace nagd Allah ya saka da alkairi yace amin munde zakiyi reporting nace to.

     Monday 8am
Na fito cikin shiri na shiga nayiwa aunty rahama sallama yauma as usual ta farfadi bakaken maganganunta Wanda idan da sabo na saba. Naje nayi reporting principal ya bani js3 da ss1 na ringa daukar su English, naji dadin kasancewa da yaran sosai, daga fara zuwana har mun saba dasu. Tunda na fara zuwa aiki na rage shiga damuwa sabd ko rahama ta bata min rai INA haduwa da students dina sainaji na manta.

      3 months later
Na goge sosai da teaching malamai da students din sch din kowa sona yake na saba sosai da sch din. Yauma as usual yara sun fita break mu kuma muna staffroom muna ta hira dasu malama halima principal ya aiki a kirani ina zuwa naga fuskarshi a cikin damuwa saida yayimin nasiha sanan ya mikomin takarda a envelope yace daga ministry of education ne aka aiko ya bani sun sallame ni daga aiki sabd sunyi bincike sun gano ni ba yar asalin jahar Kano bace, saidai idan zanyi casual

Maman Aysha
[9/15, 18:48] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
6⃣0⃣➖6⃣5⃣

Innalillahi wa inna ilaihir rajuun kawai na Iya fada sana na karba dama da bag dina a hannuna sbd haka INA fitowa daga office din PC mota ta kawai na shiga na tafi gd, direct part dina nashiga na fara kuka kamar raina zai fita waye yayi min wanan abin? Waye yasan niba yar asalin Kano bace, kuma me natare mishi? Haka na wuni a kwance band aikin kuka ba abinda nake matar gdn ma batasan na dawo ba. Sai wajen 6:30 lkcn na tabbatar elbash ya dawo yaci abinci sanan na kirashi a waya ya najin muryata cikin kuka ya mike a zabure rahama ta Dora kanta a ciyarsa besam lkcn daya dauke ya tashi ba tana tambayarsa me ya faru ko takanta be bi ba ya nufi part dina yana zuwa yace meya faru naji kina kukan da kika Dade kinayi takardar na dauko na mika masa ya karfa ya karnta, shima salati ya saki, sanan yace bari ya kira dad dinsa yaji ko yasan Wanda ya fadamusu . aikuwa dad dinsa yace duputy governor ne ya dasu su rubuta sabd ba asan asalina ba, sai yace to dad ka dauke ta contract mana, bazaiyiyu ba elbash sabd ya kafa matakai akanta, ka bawa abokin naka hakuri, to shikenan dad nagode. Matsowa yayi ya kama hannuna kiyi hakuri beauty don Allah karki daga halinki akan wanan abin, nayi miki alkawari zan nema miki aiki a company, idan company ni ne bashida damar da zaisa a koreki kinji nace to, zanyi tafiya zuwa abj gobe kwana uku zanyi, idan na dawo zansan ya zaayi nace to nagd ban karasa maganar ba kuka yaci karfina kamani yayi ya Dora kaina a kafadarsa yana rarrashi na daidai nan rahama ta shigo da gudu tazo ta fisgoni ta hankadani na fadi ta fara balai aidama nasan dole haka saita faru wanan Dan bazan kyaun nata dole ya rudeka aikai ba waliyi bane ni gaskiya ka dauke ta daga gdn nan idan ba haka ba wallahi saina fadawa dad dinka abinda yake faruwa ta karasa mgnr cikin kuka. Kama hannunta yayi suka tafi part dinsu yanata aikin rarrashi dakyar ta hakura.

    Washe gari
Da wuri ya shirya saida ya kara rokonta akan don Allah ta rike amanata kafin ya dawo, idan ya dawo zai daukeni daga gdn, ni kuma ya bani hakuri akan nacigaba da jure duk irin wulakancin da zatayi min kafin ya dawo nace to. Yayi mana sallama ya tafi aunty rahama harda kuka wai zatayi missing dinsa, da kyar ya lallabata yayi shiru sanan ya wuce.

         10pm
Aunty rahama ce zaune a falo ita da wata cousin dinta hadiya suna zaune suna hira dake kawarta ce dama shiyasa ta kirata tayin kwana. Lbri take bata akaina ita tarasa yanda zatayi dani, kuma ga dukkan alama mijinta sona yake, Amma yanzu na bude wuta nace bazan zauna da ita ba yace idan ya dawo zai dauke ta daga gdn nan.  Kaji shirme, aike dama sokuwa ce wani lkcn ina kike tunanin zai kaita idan ya dauke ta? Gida zaije ya kama mata suci karansu ba babbaka, kinga shikenan ya sami gdn Hutu. Nidai idan zaki bi shawarata muje ki koreta adaren nan idan ya dawo ya Tatar bata nan, kai kinaso ya bata min kenan, zai Iya sakina fa akan wanan yarinyar, dalla manta dashi tsakanin mace da miji sai Allah sai kiyi amfani da kissa ki mantar dashi, duk fadan da zaiyi kice bakisan lkcn data fita ba. Dariya tasa suka tafa wanan shawara tayi muje mu sameta. Ina kwance harna fara bacci sainaji muryarsu sama sama, na tashi na bude musu kofa suka shigo hadiya ce ta fara cewa lalle saken naki yayi yawa haka ya gyara mata daki kamar wata matar shi sanan rahama tace ke aysha inaso ki hada komatsanki a Daren nan kifar gdn nan idan kuma ba haka ba zanyiwa mahaifan elbash waya na fada musu ke karuwarsa ce ya kawo ki kike zaune, kuma nayi imani idan dad dinshi yaji saiya kusan tsine mishi, kuma dole kibar gdn Sbd haka ki zafi daya ko ki tafi batare da kin jawo masa fishin iyayensa ba, ko kuma suzo su koreki a wulakance cikin shesshekar kuka nace karki fada musu zan tafi, mikewa nayi na tattara kayana na fice muna tafe tare har mukazo inda zamu rabu, sanan nace don Allah ina Neman alfarma kiyi hakuri nabar motata anan sabd bana Iya long journey da mota, idan kk bar mota nayi aikin banza kenan, Sbd zaki dawo daukar motarki wata ran. Karki damu koda nazo bazan cigaba da zama daku ba, kuma nayi miki alkawari bazan taba fadawa mijinki ke kika Koran ba, nagode da zaman da mukayi dani,kuma don Allah ki yafe min sabd kin shiga tashin hankali a dalilna. Naja trolley na na fice daga gdn, garin yayi duhu banda kukan karnuka ba abinda ake ji ga hadari ya hado sai walkiya ake, tafiya nake Amma bansan Inda zan dosa ba addua nake Allah ya dauki raina na huta Sbd rayuwata bata da sauran amfani ni bakowa bace face annoba, Yessss annoba ce ni sabd duk inda naje guduna ake nayi zurfi a tunani har nahau kan titi ban Sani ba.

      Da gudu yake tafiya ya dawo daga wajen meeting, da motoci guda biyu kawai ya fita shi yake tuka motar da Kansa, dayar kuma body guards dinsa ne aciki be Ankara ba kawai yaji ya bige mutun cikin tsananin tashin hankalin ya fito ya dauke ta da gudu yasa a mota suka nufi asibiti

Maman Aysha
[9/17, 20:34] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
6⃣5⃣➖7⃣0⃣

Gudu yake kamar zai tashi sama, tun kafin ya kara ya sanar da family doctor nsu abinda ya faru, direct asibitin ya nufa, kafin ya karaso nurse din ta hada emergency bed, suna zuwa ya dauko ta da gudu ya shiga ciki, da sauri nurses suka karbeta suka Dora ta akan gadon, vital sign aka fara dauka sanan sukayi elevating bed din aka samata oxygen, akayi setting din cannula aka samata dextrose saline Sbd likita yace hypoglycemia ne, sun dauki blood sample na pcv da blood group, sanan akayi mata wasu allurai. Duk bayan 15 minute ake Chekiang vital sign din har suka dawo normal, pcv din nata da aka duba 28% sai doctor yace basai an kara jini ba. Duk wani emergency care an bata saidai har yanzu bata farfado ba cikin tashin hankali Mr kabeer yace don Allah Dr Abdul ka temakeni kar yarinyar nan ta mutu plisss, yace karka damu nayi mata scanning ko tasamu internal injury, Amma naga every thing is Norma so karka damu insha Allah zata farfado. Kallon guards dinsa yayi yace ina ganin Ku tafi gd ni anan zan kwana, daya daga cikin su me suna rabiu yace haba yallabai kai ka tafi ka huta ni saina kwana da ita, ba matsala rabiu kuje kawai Sbd idan na koma ma fargaba bazata barni nayi bacci ba, to shikenan yallabai saida safe Allah ya kara rufa asiri yace amin.
       Dakin da aka kwantar ta special room ne gado guda daya ne a dakin, sai kujera 3 siter, sai TV plasma da reciever sai kuma karamin fridge. Motarsa ya koma yasa wasu substaff maza suka goge jinin daya zuba akayi dis infecting wajen da sprit, sanan ya bude boot din motarsa ya dauko sabuwar jallabiya fara Sol ya koma dakin da Aysha take ya shiga ya rufe da key sanan ya shiga toilet ya cire suit din jikinshi yayi wanka, dake toilet din is very neet, sanan ya saka jallabiyar, ya fito ya kunna A/c dakin, ya kwanta akan kujera. Juyawa yayi ya kalli gadon da take sai yaji yanaso yaga fuskarta Sbd acikin duhu ya kadeta, kuma tunda suka shigo asibitin be kalleta ba. A hankali ya karasa bakin gadon yana dubawa ya ganta .amaki ya kamashi a knli ya furta Aisha Ahamad TURAKI ita na buge dama? To ina zata da tsohon Daren nan? Kuma ina motarta ta fito a kafa? Fuskarta ya zubawa ido yana kallo, a zuciyarsa yace tana da kyau sai rashin kunya, tsaki yayi ya koma ya kwanta.

Washe gari
Da asuba ya tashi yayi sallah, yayi addua sosai akan Allah ya bata lpy. Har nurse din ta shigo medication bata farka ba. Wajen 8:30am doctor ya shigo ya kara dubata yayi mata RBS yaga ya dawo normal, cikin damuwa Mr kabeer yace yanzu ya zanyi doctor karka damu any time zata Iya farfadowa. To shikenan Allah ya temakeni ma nasan iyayenta bari na kirasu na sanar dasu abinda yake faruwa, Dr Abdul yace OK, bari. naje office yace to. Wayarsa ya dauko ya fara dialing bayan anyi picking ya gaishe shi cikin girmamawa sanan ya fara masa bayanin abinda ya faru, saida ya bari ya gama sanan yace OK indai magnar Aysha kake to ba yata bace amma ni na riketa tun tana jaririya, kuma yanzu na koreta Sbd kin bin umarnina da tayi, kuma ni yau Kasan wata hudu kenan ban sata a idona ba. Idan kaga zaka temaka mata to, idan kaga bazaka temaka mata ba shikenan, nidai bani ba ita. Besan lkcn daya kashe wayar ba sabd tsananin mamaki ya kara maimaita mgnr a zuciyarsa bashi ya haifeta ba? Taki bin umarninsa? Kuma bashi ba ita? To meke faruwa da Aysha ne? Matsawa jikin gadon yayi har yanzu tana nan a yadda ya barta nan take yaji tausayinta ya kamashi

Maman Aysha
[9/18, 12:50] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
7⃣0⃣➖7⃣5⃣

Ya Dade yana kallonta , sanan ya fita zuwa office din Dr Abdul, doctor inaso naje gd nayi wanka, so don Allah wa zaka bani ya zauna da ita kafin na dawo? Zan yiwa nurse luba magna, to shikenan, cikin muryar damuwa yace amma Doctor ina tsoron kar wani Abu ya sameta, tun jiya fa rabonta da abinci, ai da tausayi. Dariya doctor yayi, Mr kabeer ko itace amaryar tamu ne? Naga ka damu da yarinyar sosai, aa wallahi kawai dai INA tausayinta ne, to karka damu zata dawo normal very soon, is alright bari naje na dawo, to shikenan saika dawo. Diriver shi ya aika gdn mum dinshi aka karbo masa break fast yayi wanka yaci abinci sanan ya Dan kwanta sabd jiya beyi baccin kirki ba, duk bayan yan mintuna yana kiran Dr Abdul yaji ko ta farfado, amma har yanzu shiru.

6 hours later
Zaune yake office din doctor cikin tsananin tashin hakli yake cewa Dr Abdul karfa yarinyar nan ta mutu baka sani ba, ace mutun tun jiya har yanzu fata farfado ba? Kafin yayi mgn phone dinsa ta fara kuka yana picking yace ta farfado?  alhamdulilla muje Mr kabeer patient dinka ta farfado, da sauri suka shiga dakin likita ya karayi min wasu allurai, sanan yace a bani abinci naci nidai binsu kawai nake da kallo adon gari kawai na gane acikin su to me me yasa aka kawoni nan? Me yahadanida adon gari? Nan take brain dina ta karantomin abubuwan da suka faru, bansan lkcn da nasaki wani irin kuka ba adon gari ne ya kama hannuna ya rakani toilet, ya bani sabon brush da MacLean nayi brush, sanan ya had amin ruwa ya fita nayi wanka, kafin na fito naga ya ajiyemin lotion da perfume da kuma wata shegir bul gown blue damayafinta ya fice, shafa man nayi sanan na dauki rigar nasa na fesa turare. Saida jikin sa ya bashi na gama shirya wa sanan ya shigo dakin dauke da yan ubansun food wormers ya dauki plates ya zubamin abincin da kansa yace na karba naci mamaki ne da kuma tambayoyi fal cikin zuciyata, saidai bazan Iya tambaya ba. Hadadden abinci ne Amma inayin loma biyu naji bazan Iya Ciba kawai sauna ajiye plate din wani irin kallo ya watsa min da bazan Iya fassara abinda yake nufi ba, sanan cikin wata unique voice dinsa yace ko bazaki Iya ci ba nazo na baki? Ya salam kawai na furta a zuciyata, wanan golden voice dinfa kodan mostly idan mun hadu da fada muke rabuwa shiyasa bansan voice dinsa ba, can't you answer me? Naji daddadar muryar shi ta daki kunnena, bani da apatite ne na bashi amsa a kasalance, OK Amma da kin daure kinci ko kadan ne, Sbd kusan 24hours kenan bakici komai ba, idan kuma akwai abinda kike sha'awa ki fada na sayo miki yanzu, nace ba komai nagode.

2 hours later
Tare suka shigo shida  Dr Abdul da Suleiman PA doctor ya kalleni yace ya jikin? Da sauki, Allah ya kara sauki nace amin, na sallame ki zaku tafi gd yanzu akwai drugs din Dana rubuta zai baki ki tabbatar kina sha kinji ko nace to, shikenan yallabai zaku Iya tafiya to nagode doctor, zaki Iya tashi ko na taimaka miki? Zan Iya, to saukko muje ina fara tgy naji jiri yana kwasata, na tafi zan fadi da gudu ya rikeni aidama nasan bazaki Iya ba shiyasa na tambayeki, tallafoni yayi muka karasa har bakin mota ya bude min na shiga sanan ya zagaya ta daya bangaran ya zauna Suleiman PA ya zauna a gaba, driver ya tashi motar muka fita daga asibitin gabana banda faduwa ba abinda yake, Sbd ina tsoro kar ya maida ni gida phone dinsa ce ta fara kuka yana dauka yace hlo Yaya Salma kin wuni lpy? Lpy kalau Broz, ga babynka ta dameni da rigima wai yau tru out baka kirata ba, ayya bani ita hlo my baby stop crying, ko kinaso nima nayi kuka? Aa na daina, yauwa gud girl, to uncle yaushe zakazo very soon zaka sayomin ice cream? Har chocolate zan kawo miki, thanks uncle bazan kara kuka ba yawwa gud girl saina zo  bawa mamanki, hlo my sis nayi missing dinku da yawa wallahi may na shigo abj next WK, I miss you too Broz, OK saika zo dama inason ganin ka nayi maka budurwa idan kazo mayi mgnr, wata yar iskar dariya yayi yace gud nyt. Driver ne ya juyo yace yallabai ina zamu? Kaimu gd, muna zuwa ya matsa remote katon gate din ya bude muka shiga, shi ya temaka min muka shiga har cikin gdn fadar kyau da tsarayuwar gdn bazai yiyyu anan ba, nidai nace Allah ya yi mana arziki na halal. Wani daki ya shiga dani na zauna a bakin gado sanan ya kalleni me kike shawa akawo miki kici? Nayi shiru, Aysha dake nake magana fa wayyo Allah nace a zuciyata mutumin nan yana Neman kashe ni da unique voice dinsa Ashe wasu irin qualities yake dauke dasu shiyasa yan mata suke manne masa? Can't you answer me? A firgice nace ice cream, wani shu'umin kallo ya watsamin ice cream abinci ne? Mostly idan nasha da cake shikenan ba saina ci abinci ba, fita yayi ya kawo min da cake din ya fice, nima ina gama saha na kwanta

Maman Aysha
[9/18, 14:31] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
7⃣5⃣➖8⃣0⃣
Ban farka ba sai asuba, ina tashi nayi alwala nayi sallah dake yasa an shigo min da trolley na saina bude na dauko alkur'ani na fara karatu daga yussabihu zuwa kasa, a massalacin gdnsa yayi sallah dake akwai liman yana biyansa duk wata so har makotan gdnsa ma suna zuwa sallah massalacin. Yana shiga falon yaji kira'arta me dadin gaske tana tashi kawai saiya samu waje a falon ya zauna yana bin surar da take a hankali dake shima ya sauke. Haka yaita bin duk surar da take karantawa har saida nakai suratul nazi'at, kawai sai kuka yaci karfina nan take na fara addua ya Allah kafi kowa sanin halin da nake ciki bani D's kowa, Allah kafi kowa sanin ba wani mutun da zan Iya nunawa a matsayin Dan Uwana na jini, ya Allah ka Sani tunda nazo duniya banji dimin da yakeji agun mahaifiyarsa ba, idan har iyayena sunada rai ya Allah kai gaggawar hadani dasu, idan kuma basa raye kayi gaggwar daukar raina na bisu inda suka tafi kuka sosai nake da har nakasa control din kaina. Ji nayi an rukoni, ina daugowa muka hada ido dashi Aysha me yasameki? Ko jikin ne? Nace aa, to fadamin me ya faru? Nace ba komai are you sure ba abinda yake damunki nace eh, to karna kara jin kukanki kinji? Nace to. Yana fita naje nayi wanka nasa wasu Riga da siket na atamfa, pink and white ne kalar atamfar saina dauki hijabi pink nasa, na dauki hand bag dina daya hannun kuma naja trolley din na fice daga dakin a falo na sameshi ya zabga uban tagumi nace ni zanje na tafi, nagode da temakon da kayimin Allah ya saka maka da gdn aljanna. Harna juya na fara tafy naji yace Aysha tsaya, cak na tsaya ba tare da najuyo ba wane irin sauri kike zaki tafi baki karya ba? Daga tafiya na dawo ne ko gd banje ba ka bugeni, so nasan yanzu hankalin yan gdnmu dole a tashe yake, yess I see, hanklinsu yana tashe Amma ko media basu bada cikiyarki ba yau kwana biyu? Zo ki zauna akwai mgnr da nake so dake, banyi musu ba naje na zauna, sanan ya dubeni yace baki mamaki ba dana taho dake gdn, instead of na wuce dake gdnku? Yaci gaba da magana washegarin ranar da abin ya faru na kira dad dinki nayi mishi bayanin cewa na bugeki da mota kina asibiti unconsciousness, me makon ya tausaya yanda kowanne uba yakewa dansa idan Abu ya faru, saiya jefeni da wasu maganganu da nake son jin amsarsu daga gareki, Aysha zan tambayeki bana son kimin karya, Sbd ba mutumin dana tsana irin munafiki, makaryaci da kuma me cin amana, so pliss I want you to tell me d truth. Tambayata ta farko wane irin umarni  dad dinki ya baki kika ki yi? Yace rabonsa dake kusan wata hudu kenan, a gdn wa kike bayan kin bar gdnsa? Sanan daga ina kike lokcn dana kadeki? Cikin nutsuwa na fara bashi lbri tun daga ranar da deputy governor yace yana sona, korata da daddy yayi, zama agdn elbash aikin dana fara da kuma korata da matar elbash tayi Wanda shine sanadiyar fitowata harka kade ni. Saida ya zubda hawaye don tausayi sanan yace kin tabbata lbrn da kika fadamin gasky ne? Nace eh, yace to karki damu naji duk adduar da kikayi dazu bazan boye miki ba da natsaneki Sbd rashin kunyar da ki kayimin, da kuma tozartani da kikayi a media, Amma yanzu na hakura kuma zan temaka miki, zan baki daya daga cikin gdajena ki zauna, zan nemo miki wata tsohuwa data tafa aiki a gdnmu mutuniyar kirki ce Ku zauna tare, sanan zan daukeki aiki a matsayin sakatariya ta, Amma inaso ki tsare mutuncin kanki. Insha Allah zanyi nagode Allah ya saka da alkairi, amin, idan yaso Monday saiki fara fita

Maman Aysha
[10/14, 9:52 PM] Chopy: [9/20, 10:13] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
8⃣0⃣➖8⃣5⃣

A ranar yaje gwamai ya dauko baba mero, ya direct gdn daya bamu mu zauna a lamido crecent ya wuce da ita ya sami almajirai suka tayata gyarn gdn, sanan yaje mall dinshi ya iyo mana provision, duk wani Abu da Kasan ana bukata a gd adon gari ya sayo mana, har detergents saida ya siyo, ya sayo mana gas cooker da cylinder saida ya tabbatar komai yayi normal sanan ya dawo gd. Ni kuwa tunda ya fita nake bacci ban farka ba sai after 3 toilet na shiga nayi wanka nayi alwala INA sallah naji motsin shigowarsa, bayan na idar nayi addua saina fita a dinning na same shi har yayi wanka yasa wasu shegun blue shirt da black jeans saida na Dan rusuna nace ina wuni? Ba tare daya kalleni ba yace lpy INA gajiya, ya jikin? Nace da sauki hankalinsa gabadaya akan phone dinsa yake, shiyasa na sami damar kare masa kallo wato bayan fitinanan kyaun da yake dashi, yana dauke da wani sirri da saika Tara maza dari baka sami guda daya me irinsa ba, in fact kyaun shi is very unique......ke meye kika zuba min ido kina kallona ina ta mgn ba responding? Kunya ce ta kamani na rasa me zance masa, bismilla zo kici abinci nace to a kujerar gefensa na zauna, tunda na zuba abinci bancin banci yakai 3 spoon ba sai wasa da spoon din kawai da nake Sbd tsananin kwarjini da kuma kunyarsa da nake ji, inajin ko ganewa yayi sainaji yace koma daki tunda ba zaki Iya ci a gabana ba, aikuwa da sauri na mike ina tafiya kmr wacce kwai ya fashewa a ciki na shiga daki naci, bayan na gama na shiga kitchen zan wanke plate din yace na bari me aikinsa zai wanke, dake duk masu aikin gdnsa mazane. Ina zaune ina kallo a laptop dina ya shigo dakin ni xan fita, sbd inada meeting yanzu. kamar yadda na fada miki na dauko baba meron tanacan a gdn so ki hada kayanki nayiwa bala driver mgn zai kaiki karbi wanan ya miko min wrappers din 1000 guda biyu, Ku biya ta boutique ki sayi kayan da zaki ringa zuwa office dasu, dakai food items gdn idan da akwai abinda babu kayimin magana, ina phone dinki nasa miki no na, phone dina a kashe take Sbd inaso na canja layi saidai na rubuta a paper. Be quick da Allah sauri nake da hanzari na dauko yana fadamin harna rubuta, sanan yace 9am nake fita office, so iam expecting you b4 nine kuma bana son late coming be jira abinda zance ba kawai ya fice daga dakin wata sansanyar ajiyar zuciya na saki dole kayi abinda yafi haka ma, Sbd Allah ya baka duk wani Abu da Dan Adam yake bukata a duniya, ba abinda ka nema karasa gabadaya voice dinsa ta tafi dani, Sbd gashi dai da harshen Hausa yake min magana, amma yanayin yanda yake pronouncing kowacce kalma saika rantse ba Hausa yake ba. Me karatu kar kuga kamar na zake da yawa, wallahi adon gari ya hadu ne sosai, is not my fault yanada fitenannan kyau ne, kuma ga class shiyasa

Maman Aysha
[9/20, 16:34] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
8⃣5⃣➖9⃣0⃣

Ta wani B classic boutique nabi na sayi kaya masu kyau, Amma gown sunfi yawa aciki na debo haddadun shoe & bag sanan muka wuce lamido crescent inda sabon gdn yake. Muna zuwa me gadi ya bude mana gate muka shiga, gida flat house ne me kyau anyi interlocking gdn gabadaya, kuma yanada packing space da zaa Iya ajiye motoci 4, Dan madaidaicin falo ne dauke da arch  guda  biyu, na bangaran gabas dauke yake da corrido sai dakuna guda biyu suna kallon juna da toilet a tsakiya, na bangaran yamma, kuma one bed room ne da toilet aciki da alama a matsayin master room akayi bangaren arewa kuma dinning area ne da kuma kofar ketchen gdn yayi kyau sosai, ga unguwar very silent ba hayaniya.

  Wasu yan madaidaitan kujeru yasa lemon green, so komai na falon lemon green ne, sanan gabadaya 3 bed room din ya zuba furniture's aciki, da alama bakinsa da yake saukarwa da agdn. Malam bala da baba megadi ne suka shigamin da kayana ciki, dakin da yake a matsayin master room na zaba a matsayin dakina, kuma baba mero ta tareni da faraarta.

2 days later(7:45pm)
Zaune muke muna rangada hira nida baba mero sbda matar tanada tsananin kirki ga barkwanci duk lkcn da muka zauna saita bani dariya, yau kwana biyu kenan da fara zamanmu amma kamar mun shekara da ita. Tana bani wani lbri inata dariya ya shigo gdn yanata sallama bamuji ba, har saida ya shigo cikin falon wata night gown ce me laushi a jikina, doguwa ce har kasa kaina ba dankwali saida na raba gashin gida biyu na tuke su sun kwanta a gadon bayana. Fuskarsa ba yabo ba fallasa saida na rusuna na gaishe shi sanan yace kinsan gb zaki fara fita ko nace eh, to abinda ya kawoni na manta ban fada miki address din wajen ba, Sbd state government ta karfi hayar BAGAUDA house, na koma kamfanina na club road, nace to, kinsan wajen ne? Eh mun taba zuwa Neman ka wajen daga office din mu OK to nan zaki goben har yanzu baki sayi sim card din? Nace aa, ga wani saiki yi amfani dashi Sbd da kinada waya da bansha wahala nazo ba, juyawa yayi yace baba mero ya gdn ba matsala dai ko? Tace wallahi ba komai, don Allah dama inaso na fada miki karki bari mum dina tasan kuna nan, sanan don Allah ki kula da Aisha sosai kamar yadda zaki kula da yarki, ki dauke ta a matsayin ya kuma ki kula da tarbiyar ta don na fuskanci kanta yana rawa. Ke kuma Aysha inaso ki dauki baba mero a matsayin Uwa, kuma kiyi mata biyayya banason rashin kunya kinji ko don nasan baki da kunya. So ni zan tafi saida safe muka amsa da Allah ya kaimu. Baba mero ce tace ke Aisha haka ake bazaki tashi ki rakashi ba, dariya nayi nace ni awa zan rakashi? Tab kinaso ya wulakantani kenan, wane irin wulakanci? Ba saurayinki bane? Aa wallahi ba abinda yake tsakanina dashi tausayi na kawai yake , to ai saida so ake samun tausayi, aa baba mero kibar wanan maganar, yaga ina bukatar taimako ne kawai, saiya temaka min zanje nayi sallah na kwanta gobe tashin wuri zanyi
[9/20, 20:02] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
9⃣0⃣➖9⃣5⃣

A bangaren elbash kuwa yana dawowa gd ya sami aunty rahama tana jiki duk a sanyaye, yace rahama me yake faruwa naga kamar baki da lpy, dariyar yake tayi sanan tace kalau nake, muje kayi wanka kaci abinci yace to, a daddafe yayi wankan Sbd gabadaya hankalinsa yana gun Aysha ya matsu yaje yaga halinda da take ciki, tunda ya isa abuja yake Neman ta a waya be sameta ba, kuma ya kasa tambayar rahama Sbd kar ranta ya baci. Harta jire masa abinci akan dining zai fara ci kenan saiyaga bazai Iya cin abinci ba tare daya ganta ba, kawai saiya mike rahama INA zuwa bari na duba Aysha don Allah, nan take ta saki kukan munafirci Aysha fa yau kwananta uku rabonta da gdn nan, nayi duk Iya kokarina naga na nemeta Amma na rasa, kuma ba Wanda yasan lokcn data fita da naga motarta tana nan nayi zaton itama tana ciki, saida na duba dakin naga wayam. Tunda ta fara mgn yake salati, daga karshe kawai saiya fashe da kuka idan ma guduwa Aysha tayi to kece sila, jikina yana bani abin kikayi mata ya bata mata rai harta bar gdn. Me yasa rahama? Meyasa kika fiye son kanki da yawa? Me yasa kika bar zuciyrki ta bushe kika zama marar imanin da kika kasa tallafawa rayurwarta? Bata da kowa fa, kuma ni kadai ta aminta dashi a garin nan yanzu wa yasan inda ta tafi? Why pliss itama kuka take sosai tabbas ni nayi silar tafiyarta, Amma wallahi nayi regretting don Allah kayi hakuri ina masifar sonka kishi ne yasa na aikata don Allah ka yafemin zama tayi tana rasgar kuka kana kallon ta zaka San tayi nadama, kamota yayi ya rungemeta ajikinsa yace shikenan daina kuka Allah yasa ta fada hannun nagari, kuma Allah yasa haka shine mafi alkairi a gareta rahama tace amin.

      Yau kwana na biyu kenan da fara fita aiki, kuma ba wata matsala inayin aikina succefully,  ya kafa matakan tsaro sosai, Sbd sai an tsallake office hudu sanan azo nawa, office na farko screening din mutun ake a tabbatar baya dauke da makami, harmu sttaf din wajen akewa, office na biyu kuma body guards dinsa ne suke zama physically suke checking din mutun, idan basu yadda da mutun ba tunda daga nan suke korarsa, sai office na uku kuma anan ake duba sunan mutun aga idan da sunansa acikin list din Wanda zai gani a ranar, office dina ne na karshe ni kuma duk Wanda yazo zan mishi waya na fada masa idan ya amince saiya shiga.

Zaune yake a office yana signing wasu files kawai sai wayrsa ta fara ruri yana dubawa yaga deputy governor ne yace yallabai ka wuni lpy? Lpy kalau, Aysha Ahamad TURAKI ta dawo company ka da aiki, Sbd haka inaso ka kureta yanzu nan, to yallabai tayi wani lefin ne? Umarni nake baka, baka da right din da zaka Sani na koreta yallabai Sbd kamfanina ba a karkashin gwamnati yake ba idan zan koreta ni zanyi raayi da kaina ba wani ne zai Sani ba, kuma yarinyar tana tsananin bukatar taimako banga abinda zaisa a koreta ba. Idan maganar da nayi ta bata maka rai kayi hakuri bissalam. Yana katse kiran ya fara dialing no me girma governor yayi na farko baa dauka ba, yana kara dialing aka dauka governor yana tsananin son adon gari Sbd aminin babansa ne, kuma yanada amana. Bayan sun gaisa ya bashi lbrn abinda ya faru tsakaninsa da duputy, yace to ba matsala kazo around 8pm sai muyi mgn, yace to Abba nagode

Maman Aysha



[10/14, 9:52 PM] Chopy: [9/21, 16:33] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
⃣9⃣5⃣➖1⃣0⃣0⃣

Yaje ya sami governor yayi masa bayanin komai a tsunake, me girma governor ya tausayamin sosai, kuma yayi masa alkawari zai dauki kwakwaran mataki akan shi. Adon gari na fita daga government house me girma governor ya kira deputy da chairman din partynsu, da kuma wasu mutun biyu masu fada aji a party din sunyi mishi warning sosai akan ya fita harkata, kuma sun fada mishi duk abinda ya sameni y kuka da Kansa, ya bada hakuri kuma yayi alkawari bazai kara ba.

      Yauma as usual ina office banda aikin tunanai ba abinda nake, maganar da mukayi da baba mero ce ta dawo min kodai da gaske adon gari sona yake? Sbd caring Da yake nunamin yayi yawa, kuma naga baya shiga harkar yan mata aikuwa idan da gaske adon gari yana sona nafi kowa saa wani lallausan murmushi nayi, sai wata zuciyar tace min kinga Aysha kar ki zake da yawa tausayin ki kawai yake mutumin daya hada duk wasu qualities da ake nema ajikin da namiji me zaiyi da marar asali irinki. Nan take na dawo hayyacina tabbas gaskiya zuciyata ta fadamin, elbash ne ya fadomin a rai Allah sarki ko ya yaji da yazo ya tarar bananan? Phone dina na dauko na fara dialing no dake sabuwar no ce harta katse be dauka ba, saida na sake dialing ya dauka yana jin muryata yace Aysha INA kika shiga INA ta nemanki? Kina Kano ne, ko kin tafi wani garin? Kuma a gdn wa kike yanzu ko kin sami parents dinki ne? Mikewa nayi na tafi ta wajen window na fara bashi lbrn abinda ya faru tunda ga ranar da nabar gdnsa har zuwa yanzu. Kina nufin kina kano? Eh OK to zanzo na sameki a office din gobe nace to shikenan, awaiting call ne ya shigo phone dina har three missed call INA dubawa naga Mr kabeer da sauri na dauka, shigo office dina yanzu nace to, INA shiga naga wasu  mata guda biyu dayar sanye take da uniform din yansanda, dayar kuma kana ganin ta zakasan gayu ya ratsa ta, suna tsaye abakin kofa kafin nayi magana yace da wane Dan iskan kike waya har wadanan useless din suka shigo min office batare da naba da izini ba? Rasa amsar da zan bashi nayi Sbd bansan lkcn da suka zo suka wuce ba. Kallon su yayi yace ke nazlee Kike kowa, inaso kisani bana sonki, har abada bazan taba sonki ba, kuma wallahi na kara ganin kafarki a wajena saina saba miki, kuka ta fara haba adon gari don Allah, meyasa kake wulakantani Allah ne ya jarafceni da sonka ka tausaya min mana, cikin tsawa yace nace ki fice min daga office ko sai nasa anfitamin dake, da gudu tafice tana kuka woman police din da suka shigo tare ta bita da sauri. Ba tare da ya dago ya kalleni ba yace ke kuma baki amsa min tambayata ba? Voice dina tana rawa nace uhmm....elbash ne, aiki kika fito yi ko soyayya? Wallahi ba saurayi......dalla yimin shiru be shafeni ba idan ma sonki yake, nidai abinda nakeso ki gane shine karki ga na baki na baki gd, kuma INA nuna miki caring kiyi tunanin ko kinada wani matsayi ne a wajena, your nothing tausayin ki kawai nake, so duk abinda nake miki sadakatur jariya nake Sbd haka ki dauki kanki a matsayin ke ba kowa bace face staff dina, matsayin ki dayane da duk wani ma'aikaci dayake aiki a karkashina, kuma wallahi idan kika kara barin wani ya shigo bada izinina ba sainayi punishing dinki, idan zakiyi soyyayar ki bari idan kin koma gd kyayi, I hope you get me right? Tunda ya fara fadansa nake kuka, dakyar na Iya ce masa eh, sanan yace fita ki bani waje na juya na fice jiki ba kwari. Kujerata na koma na Dora kaina akan table inata aikin kuka saida nayi me isata sanan na shiga toilet na wanke fuskata INA fitowa naga wani had some saurayi a tsaye kana ganinsa kasan he is smart muna hada ido yace min kabeer yana nan kuwa? Nace eh wa zaa ce masa? Kice marwan ne, OK phone din da na saba kiransa da ita na dauka na fara dialing yana dauka na fada masa yace ya shiga, juyawa nayi nace yace ka shiga wani mayen kalau ya bini dashi, sanan ya wuce. Yana shiga yace adon gari kana sha'aninka, a ina ka sami wanan beautyn?  kuma dan iskanci ka barta a matsayin sakatariyarka  is she not a graduate? Graduate ce mana, mafioso tayi aiki a kusa dani ne,  tayi aiki a kusa dakai kana sonta ne? Ba wani so inaso na kare mutuncinta ne, Sbd idan tana kusa dani zansan duk wani move dinta. To tunda baka sonta ni ina ciki sabd gaskiya she is beautiful kuma tanada class Kasan harna gama tsayuwa ta a wajen bata naga kai ta kalleni ba, saidai is lyk kamar tayi kuka naga Golden eyes dinta sun Dan kumbura, ko Kai ka bata mata rai? Bansan ba, Kasan bana son surutu da yawa don Allah ka fadi abinda ya kawo ka, OK zuwa nayi mu tafi gdn kaci abinci, nasa anyi maka favourite dinka, kamar Kasan yunwa nakeji kuwa, bari na fadawa mum karta aikomin da abinci yau. Tare suka fito suna hirarsu suna dariya ni zantafi ki rufe office din ki tafi, nace to, marwan ne yayi min wani lallausan murmushi yace bye Aysha, nace OK bye.

Maman Aysha
[9/22, 13:25] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
1⃣0⃣1⃣➖1⃣0⃣5⃣

Ina fitowa naga hadari ya hadu a garin har an fara iska ina tsayi INA jiran me keke napep kawai saina ga wata shegiyar mota ta faka a gabana aminci Allah ya tabbata a gareki ranki ya Dade, sunana Barr Faisal, na Dade INA Neman ki Allah be hadamu sai yau idan bazaki damu ba don Allah ki shigo na baki lift sbd inaso nasan gdnku. Bana bukatar taimakonka don Allah mallam ka tafi, nima don Allah ki taimaka ki saurareni, ni masiyinki ne ba makiyi ba pliss, wallahi na Dade INA sonki, yayyafi naji anfara sai kawai na hakura na shiga muka tafi daidai lkcn kuma motar marwan ta fito, Mr kabeer yana gdn gaba, marwan ya kalli Mr KB yace kare mata mutuncin da kake ya tashi a banza indai a commercial car zata ringa yawo, yanzu haka wanan guy din yanzu ya fara ganin ta, amma kaga yayi convincing dinta ta shiga motarsa yarinyar nada shu'umin kyaun da duk haduwar namiji saiyaji yana sonta, so you have to be very careful, cikin bacin rai KB yace bisu abaya muga INA zai kaita. Haka sukayi ta binmu har kofar gd munyi exchanging no dashi sanan na shiga gd, saida suka tabbatar ya tafi sanan suka dau hanyar gdn marwan.

6:15pm
Kwance nake akan gado abin duniya yayi min zafi, tunanin mum dasu junior ya addabeni yanzu shikenan dad ya rabani dasu? Allah sarki mum, koda wasa bata taba nunamin ba ita tahaifeni ba duk so da kaunar da take nunamin tashi daya mun rabu, ko ya takeji a zuciyarta? Gashi na kira layinta baya shiga, daidai nan naji Kira ya shigo wayaata INA dubawa naga elbash ne, hlo ka wuni lpy? Lpy kalau na matsu na ganki bazan Iya jira harsai gobe ba, so yanzu haka INA kan titin lamido crescent yimin kwatancen gdn, nace to inayi masa sai gashi har kofar gdn, saida na fadawa baba mero sanan na fita, fararen kujeru na ajiye muka zauna a compound din gdn, yana kallon fuskata ya gane nayi kuka, wato har yanzu baki daina kuka ba ko beauty? Wallahi tunanin mum dasu basma ne yaki ya fita a zuciyata, kuma abinda yafi damuna shine idan na kira layinta baya shiga, aikuwa akwai yar matar babanta a office dinmu, Bari na kirata ta turomin sabuwar no ta. Aikuwa yana mata magana ta turo masa Sbd sonshi take, yana bani na fara dialing, bugu biyu ta dauka inayin magna ta fashe da kuka nima kukan nake saida mukayi me isarmu, sanan take fadamin dad ya maida ita abuja Sbd ni, kuma shi ya canja mata layi, nima na Bata labari tun daga ranar da nabar gdnsu har zuwa yanzu in brief ta tausayamin sosai na tambayata su basma da junior ta basu muka gaisa tace kullum sai sun tambayeni sai nace musu kina makarnta, mun Dade muna fita da ita kafin muyi sallama, na Bata hakuri akan ta kwantar da hankalin ta nima yanzu bana cikin matsala hankalina a kwance yake. Cikin farin ciki nacewa elbash nagode Allah ya saka da alkairi, wallahi bakaji yanda naji dadi ba, daidai nan me gadi ya bude gate adon gari ne ya shigo gdn sanye cikin orange shirt da black jeans gashinsa ya kwanta yayi lub, ga wata iska me dadi da take kadawa fuskarsa ba walwala ya karaso wajen ya mikawa elbash hannu sukayi musabaha, ko kallon inda nake beyi ba ya shiga ciki elbash ne yace Aysha ni zan tafi kici gaba da hakuri kinji nasan halinsa yana da miskilanci dariyar yake nayi nace la karka damu wallahi ka gaida aunty rahama yace to zataji insha Allah. Gabana yana dukan uku2 nayi sallama na shiga na same she suna ta hira shida baba mero, ita kadai ce ta amsa min sallama, Amma shi ko kallona beyi ba saida na rusuna na gaisheshi kamar yadda na saba, Amma da kyar ya amsa min ina ganin haka kawai saina tafi daki, INA shiga ya biyoni Ashe ke yar iska ce bansani ba? I don't think lbrn da kika bani gaskiya ne, Sbd na fuskanci kinada rawar kai, wato kin fara Tara maza ko? Cikin sanyin murya nace elbash ne fa, eh nagani elbash ne, Wanda yayi dropping dinki dazu kuma fa? Rasss naji gabana ya fadi.......ko aure kike so? Still banyi magana ba, bazan hanaki soyayya ba tunda bani zan aureki ba, Amma inaso kisani bana son shashanci da rashin kamun kai, ban yarda ki ringa Tara min baza agida ba Sbd haka ki fadawa elbash din ya turo iyayensa wajena muyi maganar aure tunda shi yasan ko ke wacece, zai yadda ya aureki ko besan asalinki ba. Wanan shine last warning dazan baki car key ya wurgomin kan gadon, ga keyn motar da nazo da ita yanzu nan, na barmiki ki ringa zuwa wajen aiki, gud bye. Tunda ya fara magana nake kuka harya fice ya Allah ka kawomin hanyar da zanga iyayena cikin ruwan sanyi ko a daina yimin gori, saida nayi me isata sanan na shiga toilet nayi alwalar sallar magrib.

Maman Aysha
[9/22, 18:32] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
1⃣0⃣5⃣➖1⃣1⃣0⃣

Washe gari da wuri na tashi na shirya cikin pink lace nayi dauri me kyau, nasa costume masu kyau, da dauki pink shoe & bag na fice,  a motar da KB ya kawo min Mercedes 4matic 240 na tafi, INA zuwa na sami waje na faka motar, tunda na fito Mutanen cikin gun suke bina da kallo har na wuce office dina, Sbd bana shiga harkar kowa acikin wajen. Na zauna befi da 15 mint ba saiga shi ya shigo cikin wasu lafiyayyun suit fuskarsa manne da karamin farin glass din da yake kara masa kyau mikewa nayi nace gud morning sir morning kawai yace ya shiga office, ni kuma na koma na zauna naci gaba da aikina.

     12pm
Ina zaune saiga wata kyakyawar budurwa ta shigo da body guards dinta har guda uku at least zataban 6yrs direct kofar office din KB ta wuce da hanzari na sha gabanta bewar Allah baa shiga sai anfada masa, wani kallon wulakanci ta watsa min ke kuma wacece? Kodan naga alamar ke bakuwa ce shiyasa baki sanni ba, aini banida Katanga da shiga office din ina shiga ne duk lkcn danaga dama. Kiyi hakuri nafadamasa Sbd zaki Iya jamin matsala, tsawa ta daka min dalla yimin shiru bansan ya akayi ya kwasoki ba ma, I must talk to him ya zama dole ya koreki wallahi stupid kawai, hayaniyar da yaji ne tasa ya fito yaga abinda yake faruwa suna hada ido naga ya saki wani lallausan murmushi what a surprise? Yaushe kika shigo garin? Da muryarta kamar ta aljanu tace dawowa ta kenan naji kai nake son fara gani, kuma nazo wanan so called sakatariyar taka ta hanani shiga. Yi hakuri mu karasa daga ciki yacewa guards dinta su koma office na biyu su jirata, sanan yace min ke kuma ki kawo mata drinks nace to. Lkcn dana shiga yana zaune kusa da ita suna hira cikin nishadi yanata sakar mata murmushin sa me tsada nan take naji zuciyata tayi zafi, naji gabadaya ba hargitse da kyar na Iya saita kaina naje na ajiye mata tray din a gabanta harna juya zan tafi tace me kk nufi, dawo ki zubamin, da facin rai nace ke baki da hannu ne? Kb ne ya kalleni yace obey her instruction she is my wife to be rasss naji gbna ya fadi, na nemi yawon bakina na rasa da kyar na samu energy n zuba mata, nace gashi hannun ta kawai ta miko ba tare da ta kalli cup din ba Sbd hankalin ta akan waya yake, nayi zaton ta rike na saki cup din aikuwa lemon ya zube ajikin mayafinta. A hanzarce ta mike ta kaimin mari, nayi saurin rike hannun ta me nayi miki da zaki mareni? Inaso ki Sani kowanne mutun yanada daraja, kasancewa ta ina aiki a karkashin mijinki bazai baki damar ki wulakantani ba. Aikuwa wallahi baki isaba saukin wanke min zanyi magana yace karbi ki wanke mata, ba musu na karba na wanke a sink din toilet dinsa  saida na kade sanan na bazashi akan table din shi raina a bace na nufi kofa zan fita kawai sainaji tace banza marar asali.......Bata karasa ba ya wanke ta da mari cikin kuka tace akan wanan bastard din ka mareni? Inajin haka na fita da gudu ina kuka, Don't ever call her bastard and walk out from my office ta tsaya tana binsa da kallon mamaki cikin bacin rai yace I say out!! Tana rawar jiki ta dauki mayafinta ta fice tana kuka

Maman Aysha
[10/14, 9:52 PM] Chopy: [9/23, 13:16] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
1⃣1⃣0⃣➖1⃣1⃣5⃣
Tana fita ya zauna ya dafe Kansa Sbd be saba hayaniya ba, ya dade ahaka daga baya kuma ya dauki laptop dinsa da key ya fice ya tafi gd.

Zuby kuwa tana fita gdn wata friend dinta rumana ta nufa tana zuwa ta zube a falo tana kuka da sauri tace zuby me yake faruwa kk wanan kukan? Nida adon gari ne rumana, inayin hakuri da miskilancinsa da duk wani wulakanci da yake min Sbd INA masifar sonsa Amma yau har marina yayi Sbd wanan yar iskar yarinyar da aka gano Bata da asali, wacece yarinya kenan? Aysha A TURAKI, meye hadinshi da ita? Wai yanzu itace sakatariyarsa, kuma wallahi na tsani yarinyar kinsan tana da wani irin shu'umin kyau zata Iya kwacemin shi, kuma kinsan irin wahalar Dana sha kafin ya amince zai aureni, gaskiya kam Amma tunda hakane da makirci zaki koreta bada isa ba, yanzu ki kirashi ki bashi hakuri kinsan ance me nema baya fushi kiyita lallabashi har ki samu ya hakura, a hankali sai musan yanda zamu fillowa al amarin. Shiyasa nake sonki my friend har naji zuciyata tayi sanyi bari naje na tafi kinsan da body guards naje company nasa Amma Sbd bacin rai basu San na fito bama , bari nace musu su tafi kawai ni na wuce sai munyi waya to shikenan.

Zaune yake yana ta tunani, Allah sarki aysha rayuwarta akwai abin tausayi a ciki, ace mutun bashi da kowa ita kuma irin destiny dinta kenan, insha Allah zan rike amanarki har zuwa lkcn da zakiyi aure daidai nan phone dinsa ta fara kuka yana dubawa yaga zuby is calling... Kawai sai ya mayar ya ajiye, haka tayi ta kira har wajen 10 missed call, ko tunanin me yayi kuma? Data kara Kira sai ya dauka, ta naji yayi picking saita fara kuka don Allah sweet heart kayi hakuri, bazan Iya rayuwa bakai ba don Allah ka tausayawa rayuwata ka yafe min. Naji zanyi hakuri Amma sai kin gyara halinki, kuma kin bawa Aysha hakuri Sbd kinyi mata cin fuska,  to to na amince insha Allah zanzo na bata hakuri gb, is alright Allah ya kaimu goben, bye.

Ni kuwa tunda na koma gd INA daki saida nayi kuka me isata kallama dayace take min yawo a zuciyata "she is my wife to be" dama adon gari yana soyayya? Dama yayi dating matar dazai aura? Amma na tafka babban kuskure dana bari zuciyata ta kamu da sonshi, ya Allah ka cire min sonshi a zuciyata da wanan tunanin wani wahallalan bacci ya dauke ni ban farka ba sai after 4, INA tashi na shiga toilet nayi wanka nayi alwala nayi sallar laasar wata English gown na saka na fita wajen baba mero tace yanzu nake tunanin naje na duba naga ko lpy, Sbd tunda kk shigo banji motsinki ba dariya nayi nace bacci ne ya kwashe ni shiyasa, me kika dafa mana? Abinda kk so nayi miki, kina nufin danwake? Eh kai Amma nagode shiyasa nake kara sonki baba mero, itama dariya take  kitchen na shiga na zubo Iya yanda zan Iya ci, sanan na dawo falo inaci muna hira muna dariya, wayata ce ta fara kuka INA dubawa naga Barr Faisal ne, da sallama ta na dauka bayan mun gaisa yace kira nayi naji amsata, Aysha kinyi tunanin? Eh nayi kuma na amince da soyayyarka, alhamdulilla yace, saida, saidai me Aysha? Akwai maganar da nake so na fada maka, amma nafiso muyi face➖face, is OK zanzo in d night, yau kaina yana ciwo ka bari sai gobe, ayya iam sorry my dear Amma kinsha magani? Eh to Allah ya sauwake, bari na barki ki huta sai na kara kira bye. Ina kashe wayar baba mero tace waye wanan din? Sabon saurayi nayi sunansa Faisal, kuma kina sonsa? Sosai ma, ni kuwa sainaga duk duniya ba mutumin da kika dace dashi kamar kabiru, wallahi duk lkcn da nayi sallah sainayi addua akan Allah yasa kabiru ne mijinki Sbd halinku na tausayi da rashin kyamar mutun iri daya ne, Aysha kina da kyakkyawan halin da har yasa nake jinki kamar yata, kullum burina shine na ganki acikin farin ciki, don Allah ki amince ki auri kabiru kinji Aisha. Baba mero kenan, ke kike kidanki kike rawarki, shifa har yanzu be taba cewa yana sona ba, kuma fa yanada wacece yake so har ansa masa rana ma, maganar so kam na Dade da ganewa yana sonki, saidai da kikace ansaka masa rana shine matsalar, Allah yasa haka shi yafi alkairi nace amin

   Washe gari
As usual INA office saiga Suleiman PA ya shigo, bayan yaje sun gama da adon gari ya fito sai ya zauna a wajena muna hira saiga ta ta shigo ta dau wanka tayi kyau sosai, INA ganin ta naji gabana ya fadi Suleiman ne yace miss zubaida barka da zuwa, yauwa Suleiman ya aiki alhamdulilla da gadara ta bude office din ta shiga wai wanan zuby din a ina take ne Sulaiman? Yar gdn minister of foreign affairs ce, kuma ita yallabai zai aura in Allah ya yarda, to nazle da tazo jiya fa? Ita kuma yar gdn commissioner of police ce, lbri yake ta bani, Amma gabadaya hankalina baya tare dashi, har saida ya fahinta, sai yayi min sallama ya tafi Mr kabeer ne ya kirani a waya yace nazo yana don ganina inda suka zauna jiya yauma anan suke, dama my Queen ce take so ta baki hakuri akan abinda ya faru jiya, eh hakane, kamar yadda swit heart ya fada miki zuwa nayi na baki hakuri Sbd wallahi nayi regretting sosai don Allah ki yafemin, nace ba komai Allah ya yafe mana baki daya zuciyata tana yimin wani irin zugi da radadi na kishi ban taba sanin son adon gari yayimin mummunar illa ba sai daga jiya zuwa yau, da kyar na Iya cewa zan  Iya tafiya? Yace eh, ina juyawa wasu zafafan hawaye suka fara zuba a idona zama nayi na dora kaina akan table na fara kuka sallama naji anyi INA dagowa naga Faisal ne cikin rudani yace wat's wrong Aysha nayi sauri nace ba komai bacci nayi, lpy na ganka anan? Nazo naga Mr kabeer ne akwai wani aiki da zamuyi dashi, to bari na sanar masa, ina fada mishi yace ya shiga Ashe friend dinsa ne

Maman Aysha
[9/24, 12:12] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
1⃣1⃣5⃣➖1⃣2⃣0⃣

Yana shiga ya sami waje ya zauna yace Ashe kaida amarya ne? Yace wallahi kuwa, yau ta kawomin visit bayan sun gaisa suka tattana akan abinda ya kawo shi, sanan suka fito a tare har zuby. Ina cikin hada kayana Sbd lkcn tashi dama yayi naga fitowarsu Faisal ne ya karaso inda nake tsaye yana wani lallausan murmushi yace baby tafiya zakiyi? Cikin faduwar gaba nace eh, to muje nayi dropping dinki, thanks yau nazo da mota zubamana ido adon gari yayi yanamin kallon tuhuma, shi kuwa Faisal idonsa ya rufe yama manta da mutane a wajen, haka kawai adon gari ya tsinci Kansa da shiga damuwa, a INA Barr Faisal ya Santa? Yaushe suka fara soyayya? To ko shine yayi dropping dinta rana nan? Zuby ce ta katse masa tunani da cewa mu tafi swit heart cikin shan mur yace OK muje, A tare muka fita dasu saida ya rakani har bakin mota ya bude min na shiga sanan yamin sallama da sharadin zai zaizo bayan sallar magrib.

 Tsaye suke ajikin motar sa suna sallama da zuby, amma gabadaya hankalinsa a wajen mu yake zuby ce tace amma na fuskanci Barr Faisal yana tsananin son yarinyar nan, kallo daya zaikai masa Kasan yayi falling da yawa saidai INA tausaya masa duk ranar daya gane bata da asali....enough me yasa bakinki baya shiru? Me yasa kk da taurin kai? So nawa kk so na fada miki maganar nan ta fita daga bakin ki, Karki bari na nuna miki bacin raina Sbd zaki sha wahala be jira driver shi ya bude masa motar ba ya bude da Kansa, kafin kace me body guards dinsa ma suka shiga motocinsu yau da motoci shida ya fito, cikin few seconds sukayi arranging din moticin suka fice daga wajen, itama jiki ba kwari ta bude motarta ta fita da tunanin wulakanci irin na adon gari.

Direct gdn mum dinsa ya wuce yana zuwa ya zube akan ciyarta banda shagwaba ba abinda yake, wash Allah wallahi mum na gaji sannu my son, ai duk lefinka ne da kaki yin aure, da kanada mata da yanzu saita yi maka tausa, sauri yayi ya canja topic din zancen da me aka dafa mana yau mum? Jallop din taliya ce, ya tsani taliya Amma Sbd karya fada ta kara cigaba da zancen yayi aure sai kawai ya basar yace bari naje gd nayi wanka, dama zuwa nayi naga lafiyarki, kuma abincin fa? A koshe nake, to dama inaso na fada maka gobe zan tafi Kaduna, Kasan next WK bikin abokinka kamal Sbd haka zanje mu fara shirye2 idan na tafi gobe sai angama bikin zan dawo, gaskiya mum kinaji da Haj Asiyan nan Ku kunata zumuncnku, mu kuwa haduwa tayi wahala saidai kusan kullum sai munyi waya dashi, kuma time to time INA zuwa nagaida dad dinsu a office, kuma duk lkcn naje Kaduna sainaje gdn kanwarsa ce dai neehal rabon da na ganta tun bata fi 8yrs ba, tab ai yanzu ta zama budurwa, yanzu haka ma likita ce kwanan ta kammala karatun ta, ah dakyau, ni zan wuce idan yaso goben sai sadiq ya kaiki a helicopter dina to shikenan son sainaji ka OK bye mum. Gida ya shiga yayi wanka ya kwanta bacci

Ina shiga gd nayi sallah na shiga kitchen dama yau dambu nake sha'awa sbd azumi nake, ina azumin litinin da alhamis. Tun safe nasa  baba mero ta tanadarmin komai kafin na dawo, cikin 1hour nagama danbun, sanan na hada lafiyyayen zobo da yaji kankana, nayi potatoes bols, da paper soup din ostel dake ina sonshi sosai, kara share gdn nayi na gyara kitchen din kamar ma banyi girki ba, na kunna turaren wuta a falon sbd ya kawar da kanshin abincin, sanan na shiga wanka nasa wata orang English gown anyi shaping dinta, tayi min kyau sosai, gashina kuma anyi min twisting dake yanada tsaho ta kwanta min a gadon bayana nayi wanka da turare sanan na fito na karasa hada fruit salad
nasa a fridge

7:15pm
Nasha ruwa na gaji, kuma gashi Faisal yace zaizo kawai saina dauki phone dina nace don Allah yayi hakuri da zuwan Sbd kaina nasha ruwa na gaji gashi kaina yana min ciwo. Duk da ba haka yaso ba Amma Sbd gudun bacin raina saiyace ba matsala.

A kwance nake akan 3seater INA kallon series film din da ake Bollywood me suna Geet, baba mero kuma tana zaune a kasa tana cin dambu Sbd karar TV bamuji shigowar motarsa ba, kawai sai sallamarsa mukaji saida ya Dan jira for some seconds sanan ya shigo purple shirt da white jeans me digon purple ajiki yasa, ina kallonsa nace masha allah, allah yayi hallita anan. waje ya samu ya zauna saida na durkusa na gaisheshi, shi kuma ya gaida baba mero, kallon ta yayi da faraa yace baba mero yau kuma danbu kika yi? Aisha ce tayi wallahi, dake tayi azumi aikuwa akwai Aisha kawo masa, don naga kaima kana sonsa Sbd da kana sawa nayi maka, kallon fuskarsa nayi Sbd inaso na tabbatar da abinda take fada, sainaga yayi murmushi kawai, Amma fa ita yayiwa bani ba😀. A nutse na mike nace nan zan kawo maka ko dining? Cikin wata murya ta kasaita yace kawo min nan, a nutse na dauko flaks din abincin, sanan na dauko plate da spoon na bude fridge na dauko guntun zobon dazu da kuma fruit salad duk na Jere a gabansa kum duk lkcn Dana sunkuya zan ajiye kayan saiyaji kamshin turarena ya daki hancinsa, wani irin mayyataccen kallo yake bina dashi, har baba mero ta gane ta mike ta koma dakin ta. Da murya can kasa yacemin ba zakiyi serving dina ba? Da sauri nazo na zuba mishi I tot zaice yayi yawa, Amma sainaga ya fara ci na zuba mishi zobon a cup, yanaci yana kora zoban kana kallonsa Kasan yana enjoying cin abincin, INA satar kallonsa saida ya share dambun Tass, da Kansa ya kara zobon ya shanye, fruit salad din ne yace zai tafi dashi yasha a gd nace to mikewa yayi tare da cewa kya fadawa baba mero na tafi nace to, Bari na rike maka fruit salad bowl din. Saida na rakashi har bakin mota nasa aciki nayi mishi sallama, harna juya na fara tfy saiya tuno da abinda ya kawo shi gdn, cikin unique voice dinsa yace Aysha zo nan INA zuwa yace meye hadiki da Faisal? Da rawar murya nace sona yake, kuma kema kina sonsa? Kai kawai na daga masa, are you sure? Nace yes a hankali, to kuma Elbash fa? Aishi ba soyayya muke ba, kawaidai yana jinane kamar blood sister shi, nima kuma haka nake jinsa. Is alright saida safe, kawai ya shiga motarsa ya tafi.


Maman Aysha
[10/14, 9:53 PM] Chopy: [9/25, 12:10] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
1⃣2⃣5⃣➖1⃣3⃣0⃣

Yana zuwa gd wanka yayi ya dauko fruit salad dinsa yasha, sanan ya shiga toilet yayi brush ya hau gado ya kwanta, kyakyawar fuskarta yake hangowa a yanayin daya ganta dazu ya rasa me yasa a yan kwanakin nan yake yawan tunanin ta, dandanon girki dazu ya tunu,  meyasa yake jin kishinta sosai? Karfa ace na fara sonta? Wata zuciyar tace kul karma ka soma, Sbd mum dinka bazata taba amince maka ka aureta ba, da wanan tunanin bacci ya dauke shi

Washe gari
Wajen 12 pm mum din adon gari suka tafi kd da sadiq, ina zaune ina aiki Faisal yazo ya sami kujera a kusa dani ya zauna da mamaki nace lpy ka baro wajen aikin ka ka taho nan? Wallahi tunanin ki ne ya addabe ni, na kasa jurewa shiyasa nazo na ganki, wani murmushi ya sakar min yace yau tare zamuyi aikin. Haka ya zauna muna ta hira Sbd caring din da yake nunamin nima yanzu na fara sonsa sosai dagowa yayi yace Aysha nifa har yanzu ban taba ji kince kina sona ba, anya da gaske ana sona kuwa? Hawaye ne ya fara zuba a idona subahanalla me ya faru? Ko mgnr dana fada ta bata miki rai ne? Ko daya, ina sonka Faisal saida inaji ajikina aurena dakai ba me yiyuwa bane, Sbd duk ranar da parents dinka suka San ko ni wacece bazasu taba yarda ka aureni ba. Ban gane ba Aysha, yimin bayani yanda zan fahimta. Kaga yadda ka ganni to haka nake banida kowa, bansan kowa nawa ba, ba wani mutumin da zan nuna maka nace Dan uwana ne kuka sosai yaci karfina.....is OK Aysha ki dena kuka, koma ya kk INA sonki a haka zan samo miki iyayen karya a daura aurenmu, idan yaso koda su dad dina sun gane daga baya kinga kin riga kin zama matata, so duk yanda zasu yi dani bazan sakeki ba. Kallonsa nayi da jajayen idanuwa na nace kana ganin hakan zai yiyu? Yes me zai hana, kuma so nake muyi auren nanda 1 month, Allah ya zaba mana abinda yafi alkairi yace amin, bari na tafi zanzo in d night, nace to Allah ya kaimu tare muka fita nayi masa rakiya muna cikin tfy call ya shigo wayata, ina dubawa naga adon gari hlo sir, shigo ina son mgn dake, nace to Faisal bari na koma daga nan boss yana nemana, is OK saina zo. Da sauri na shiga office din kamshin turaren sa ne  ya bugi hancin na sanan sanyin A/C ya biyo baya. Zaune yake akan 3 seater da sallama na shiga bayan ya amsa yayi min nuni da na zauna a kusa dashi, a darare na zauna sanan yace mum dina tayi tfy zuwa kd sai next WK zata dawo, ni kuma bana Iya cin abincin restaurant idan ba ya zama dole ba, so shine nake so daga yau ki ringa zama a gd kinayi mana girki, kafin mum ta dawo kallon kwayar idona yayi Wanda har saida tsikar jikina ta tashi inafat ban takura miki ba ko? Murmushin da nasan yana karamin kyau nayi sanan nace ba matsala to yanzu ki koma gd kawai ki Dora mana abinci Sbd harna fara jin yunwa nace to a tashi lpy.

Ponded yam nayi da egusi soup, sai paper chiken, da kuma kunun aya me kwakwa da madara zuwa 3pm na gama hada komai, sai kawai na shiga wanka na shirya cikin wani boyel sky blue Riga da siket ne, sanan nayi simple make up nayi na fito baba mero sai tsiya take min wai bata gane tsakanina da adon gari ba kodai mun daidaita kanmu ne nace aa wallahi har yanzu be ce yana sona ba, tace amma ya dauko hanya ai, a zuciyata nace Allah ya amsa bakin ki.

Saida ya koma gd yayi wanka ya canja dressing as usual kanan kaya yasa, black jeans da red shirt me tsada, sai flat cover shoe red, tun kafin ya shigo gdn muka jiyo kamshin turaren sa, da fara'arsa ya shigo saida ya Dan rusuna ya gaida baba mero, sanan nima na durkusa na gaisheshi sanan nace bismilla INA gaba yana bina a baya saida mukaje har kan dining nayi serving dinsa sanan na kawo masa ruwa a bowl ya wanke hanunsa yace ni ban Iya wanan katsantar ba, sink din dining area ya nufa ya wanke anan, sanan ya dawo ya fara cin abincin saida yaci yayi dagas sanan na kwashe kayan na dawo muka fara hira, yanzu abin nasa mamaki yake bani Sbd ya daina shareni yana sakar min fuska sosai, saidai saida har yanzu mulki da kasaita suna nan, kuma idan yana magana sai ya ringa wani basarwa phone dinshi ya dauka ya kira mum bayan sun gaisa yace masa ga neehal ma Ku gaisa ta karba Yaya kabeer ina yini yana jin voice dinta yaji gabansa ya fadi, lpy kalau neehal ya gd kuma ya shirye2 alhamdulilla ai zakazo daurin aure ko? Insha Allah, to Allah ya kawo ka lpy amin nagode. Tunda ya fara wayar na shiga tunanin wacece neehal? Me yasa mum dinshi ta matsu da saiya gaisa da ita? Shi ya katse min tunani da cewa Mrs Faisal ya akayi ne? Ko tunanin Faisal din ne? Waima na tambayeki, kin bawa Faisal lbrn ki nace eh, OK to me yace? Nan na kwashe duk abinda yace min na fada masa, wata yar iskar dariya yayi sanan yace shege Faisal, kuma kin yarda da discission din da ya yanke? Nace eh, har yanzu ke yarinya ce Aysha, kuma he is a barrister you can't understand his true color zai kara magana kenan call ya shigo wayarsa hlo OK your Excellency gani nan zuwa. Aysha bari na tafi zamu shiga meeting ne da Excellency, wani shu'umin kallo yayi min yace ina ganin daga can zan wuce gd, gobe da safe ki hadamin break fast da wuri don Allah, zanzo naci kinji beauty nima yau a Dana sunan wata sansanyar dariya nayi da har saida kumatuna ya lotsa nace Allah ya kaimu gbn.

Maman Aysha
[9/25, 22:53] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓

1⃣3⃣0⃣➖1⃣3⃣5⃣

Tun ranar da mum ta tafi kd kullum adon gari a gdn yake cin abinci, dalilin haka yasa wata shakuwa ta shiga tsakanina dashi da kyar yake tafiya idan yazo.

Yau Friday, ana saukowa daga sallah direct gdn mu ya taho wata farar gezna ce ajikinsa da kudin ta zai kai 150k da bleu zare akayi masa dinkin, ya Dora wata dakyakkiyar hula me tsadar gaske anyi mata Zane da blue and white zare, abinka da farin mutun ba karamin kyau yayi ba, white rice and stew da cose low nayi mishi bayan yagama ya kalleni yayi min lallausan murmushin sa me tsada yace zan tafi Kaduna gobe daurin auran kamal ina ganin sai Sunday zan dawo akwai wani Abu da kuke bukat? Jikina a sanyaye nace ba komai Allah ya kaika lpy ya dawo dakai lpy, yace amin beauty, neehal ce ta fado min rai a zuciyata nace shikenan zaije su hadu da ita, idan kyakyawa ce ma may b ya aureta tunda mum dinsa ba sosai take son ya auri zuby ba, hawaye naji ya fara zuba a idona muna hada ido yace haba my lovely sis, ya kk kuka kuma, ko bakya so kiyi missing din brodanki? Kai na daga masa ohh sorry karki damu Faisal yana nan zan fada mishi ya kula min dake sosai kinji. A zuciyata nace Dan renin hankali ni kai nayi missing ba Faisal ba, kuma ko baka fada ba Faisal kam ai muna tare......katseni yayi da cewa ko zaki bini mu tafi tare? 😳 aa Allah ya kiyaye yace amin, lekawa yayi sukayi sallama da baba mero ya bata kyautar kudin da nima bansan nawa bane sanan muka fito na rakoshi har bakin mota.

Da helicopter dinsa ya tafi, gdn su kamal ya fara zuwa dake unguwar rimi bayan ya gaisa da mum dinsa da kuma uwar ango sanan ya wuce hotel din daya kama musu shida body guards dinsa guda biyar da kuma sadi, kowa dakin sa daban sanan sanan dukkansu saida ya bawa kowa 50k. Karfe 8 suka tafi wajen dinner wacece fadar zaruwatta ma bata lkc ne, wani lafiyyayyen boyel yasa maroon da kudinsa zai kai 250k banda daukar ido ba abinda yake  hammm me karatu just imaging wato zallar kyau ne ya hadu da daukar wanka, matasan kano sunyi gaskiya da suka sa masa suna adon gari domin kuwa ya yaki yam matan Kaduna wasu harda fada, amma shi besan ma sunayi ba 😀lol.

Washe gari bayan an daura aure wajen 4pm suka fara shirin tfy wajen mother's eve da Maman ango ta shirya, daidai nan FCT minister ya kira adon gari yace masa yayi winning contract din daya nema, Sbd haka duk yanda zaayi ya tabbatar ya isa abuja b4 8pm Sbd President zai zauna dasu 8:30, aikuwa ba shiri yayiwa ango da mum dinsa sallama ya suka wuce abj, 1 hour a abj tayi musu direct gdnsa nacan ya wuce yayi wanka ya canja kaya yayi shiga ta alfarma sanan ya wuce villa. Bai fito daga villa ba sai wajen 11pm direct gdnsa kawai ya wuce yayi wanka ya kwanta, saidai me? Tunanin aysha ya hanashi bacci kwana dayan da yayi beji daddadar muryarta, haddadan abincin ta da kuma kyakyawar fuskarta da be gani ba da kyar ya samu yayi bacci zuciyarsa fall tunanin ta

Washe gari

Tun wajen 9am ya nufi gdn Aunty Salma, lkcn daya shiga gdn shiru duk yaranta sun tafi makaranta sai yan aikin gdn da suke ta kaiwa da komowa. Wata daga cikin su yayi wa magana tace tun safe bata fito ba, yace me gidan fa tace ya fita, bed room dinta ya nufa direct ya tsaya a bakin kofar yayi knocking tana kwance tace waye? Yace ki bude mana, tana jin voice dinsa ta mike da sauri ta fito Sbd suna tsananin son junan su, what a surprise broda baka fadamin zaka zo ba a tare suka dawo falo nifa yunwa nake ji, kuma naga kamar yau ko break fast dinma bakiyi ba wallahi banida lpy ne, shima me gdn be karya ba ya fita, to ni ya zakiyi dani kenan? Bari nasa marwa ta soya maka Irish, yarinyar tana da tsafta sosai, to don Allah tayi sauri. Meyasa baka fadamin zaka zo ba? Wallahi nima un expected abin yazo min baki tayani murna ba nayi winning contract din nan ta gina estate a maitama, gidajen ministers ne, shine President ya nemi ni mu tattauna yanda abin zai kasance, to Allah ya taimaka yace amin. To ni yanzu wa zaka samomin ta tayani girki kafin na samu sauki, Kasan na shagwaba megida na baya Iya cin abincin restaurant. Inada wacce zansa tazo, idan tayi miki girki mijin naki ma bazai gane bake kikayi ba Sbd itama expert ce, zanyi waya Sulaiman ya sakota a jirgi gb, Amma fa Iya sati daya kawai zan ara miki ita, idan zan tafi tare zamu wuce. Ba matsala ai hakan maka taimaka min Allah ya kaimu goben yace amin

Maman Aysha
[9/26, 22:20] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
1⃣3⃣5⃣➖1⃣4⃣0⃣

To Amma yar gidan waye yarinyar da zaka kawomin? Iam her father, mother, broda every thing. Ban gane ba? Nan take ya kwashe lbrna from AtoZ ya fadamata, kai Amma na tausayawa mata, har naji ina sonta  tun kafin na Santa. Tunda hakane ka fadamata ta taho yau mana, idan naki fa? Pliss my broda taimaka min, kaga abbansu nana ya samu yayi break gobe kafin ya fita,  aike kullum damuwarki kenan abbansu  Nana, shikenan bari na kirata

Muna zaune a falo nida baba mero muna break fast, Sbd muma yau bamu tashi da wuri ba, kiransa ya shigo wayata, da sauri na dauka Sbd nayi missing unique voice dinsa yau 2 days bamuyi waya ba, bayan mun gaisa yace na bawa baba mero, suna gaisawa ha hadata aunty Salma suka gaisa dake sun saba sosai don tasha yi mata zaman biki ma idan ta haihu. Saida suka gaisa sosai har suka taba hira sanan yace ta bani wayar, INA karba yace don Allah alfarma nakeso kimin aysha, sister Salma ce bata da lpy shine nakeso kizo ki Dan taimaka mata da girki for 1 wk, idan zan taho saimu taho tare kinji, nace to yaushe kenan zan taho? Yau, nasa Sulaiman yayi miki booking din jirgi, idan kin shirya zaizo ya kaiki airport,  ki fadawa baba mero ta tafi gd idan kin dawo saimu dakkota  Sulaiman zai baki kudi ki bata nace to, Allah ya kawo ki lpy nace amin.

Jirgin 7pm na shga, Sbd haka 8:15 a Abj tayimin, INA sauka na tarar da driver aunty Salma yazo dauka ta muka tafi. Black Arabian gown ce ajikina, na yane kaina da mayafin rigar. Fadar kyau da haduwar gdn aunty Salma bata lkc ne me karatu kayi imagining kawai. Jiki ba kwari nayi sallama na shiga gdn, akan dining na same su suna cin abinci muna hada ido da aunty Salma kawai saita kware ta fara tari saida ya dauko mata ruwa sanan ya tsirga, wani irin kallo ta Bini dashi da har INA gaisheta amma batasan INA yi ba har saida adon gari yace sis gaisheki fa take, sanan ta dawo hayyacinta ah lpy kalau ya hanya nace alhamdulilla, marwa zo ki rakata daki, INA barin wajen ta kalli adon gari tace da ace ba uwa daya uba daya nake dakai ba da sai nace kawo yarinyar nan gdn nan set up ne,taya zaayi ka kawomin wanan kyakyawar yarinyar kamar ba mutun ba? Wata yar iskar dariya yayi sanan yace wallahi ki rage kishi, Dan nasan duk akan mijinki kike wanan abin, to tanada mijin da zata aura, kuma ita kudi ko kyau baya gabanta ballatana tayi tunanin aurar mijinki, kuma in banda abinki sister ai kema kyakkyawa ce. Ki kwantar da hankalin ki da Allah ki zauna da ita a bisa amana insha Allah ba abinda zai faru kinji my sis, tace to shikenan.

 wacece aka kira da marwa ita ta rakani wani daki INA ajiye kayana na fada toilet nayi wanka, sanan nayi sallah, har dakin aka kawo min abinci, Amma saina kasa cin komai tunanin yanda zanyi zaman gdn...sallamarsa ce ta katseni, kamshin sa ya bugi hanci na kan gadon yazo ya zauna yace min ya hanya? Banyi magana ba sai dagowa nayi muka hada ido sanan muka sakarwa juna wani lallausan murmushi a hankali ya furta I miss you my lovely sis, can kasa nace I miss you too, yace da gaske? Faisal bezo ya tayaki hira bane? Basarwa nayi kamar banji abinda yace ba, abincin da aka kawomin ya kalla yace me yasa baki ci ba? Nace na koshi, ohh sorry ashefa bakya Iya cin abinci da daddare ko? Bari na dauko miki ice cream, yana kawomin yayi min sallama ya tafi

Maman Aysha
[9/27, 10:45] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓

1⃣4⃣0⃣➖1⃣4⃣5⃣

Yana fita da few minutes aunty Salma ta shigo tace aysha bakiyi bacci ba nace eh, don Allah fa kiyi hakuri idan mun takura miki, wallahi mijina ne ba kowanne abinci yake Iya ciba, ni kuma kwana nan ba kowanne abinci nake son jin kamshinsa ba, karki damu aunty Salma ba wani Abu wallahi, to ngd sosai, naji lbrnki a wajen broda I pity you Allah ya bayyana miki iyayanki nace amin. Tun kafin kizo da naji lbrnki naji INA sonki, so don Allah ki saki jikinki ki dauke a matsayin elder sis dinki kinji? Murmushi nayi nace to nagode, to me zaki dafa mana da safe? Duk abinda kk ce, OK akwai komai da zaki bukata a kitchen din, na baki choice kiyi mana duk abinda ya samu, murmushi nayi da har saida kumatuna ya lotsa nace to. Bari na barki ki kwanta saida safe nace Allah ya kaimu. Tabbas aunty Salma tafi adon gari kirki da saukin kai, kyakyawar mata ce Sbd suna tsanin kama da Broz sosai, yau daya na fara ganinta amma sainaji ta shiga raina. Addua nayi na kwanta Sbd tashib wuri zanyi

Ina idar da sallar asuba na shiga kitchen, paper soup din kaji na farayi, sanan na soya doya da kwai da plaintain na dama kunun gyada na kwaba fulawa nayi shawrma, sanan na tafasa ruwa a kettle na zuba a flaks ko wani zaisha tea zuwa 7am na kammala komai, INA fitowa daga kitchen naga yaranta nabil da khairat sun fito cikin shirin su na makrant, marwa ce take kula dasu. Da gudu suka zo suka rungumeni nabil yace ya sunanki? Nace aunty Aysha yace zaki zauna a gdnmu? Nace eh, yace INA sonki aunty Aysha, dariya nayi nace nima INA sonku nabil da khaitat murna suka hau yi, sanan na kama hannun su mukaje na zuba musu abinci sukaci, sanan na wanke musu hannu mu kaje na zuba musu shawarma a lunch box dinsu banda surutu ba abinda sukemin, gabadaya sai tunanin su basma da junior ya dawomin sabo bansan lkcn da hawaye ya cikamin ido ba, daidai nan mum dinsu ta fito da gudu sukaje sukayi hugging nata gud morning mum tace morning my kids, kunci abincin? Eh Aunty Aysha ta bamu, kuma yau da Aunty Aysha tayi mana shawarma da ita zamu tafi sch. Dariya tayi tace dats very gud, Aysha dama kin Iya shawarma nima dariya nayi nace eh, dakyau ko catering kk karanta ne? Aa, OK to kuje Ku tafi karku makara kharat ce tace ni awajen aunty Aysha zan zauna, nace yi hakuri kije khairat idan kin dawo zan kaiki wonder land ki hau mota, nabil yace nima zaki kaini? Nace eh da gudu suka fita suna murna INA dagowa muka hada ido da Maman su ta sakar min murmushin jin dadi tace sannu da kokari aysha. Daki na koma na gyara, itama na shiga na gyara mata room dinta da toilet ita kuma ta gyara part din megidanta sanan nayi wanka nasa wata fitted gown ta wani material green, dinkin yayi min kyau sosai, simple make up nayi na murza dauri me kyau, sanan nasa sarka da Dan kunne nayi wanka da turare na dauko laptop dina na fara kallon wani film da nayi down loading wa men hubbi maqatal. Sai wajen 8 me gidan ya fito ya zauna a dinning ya kwashi abinci, da zai fita aunty Salma tazo tace naje mu gaisa dama ta bashi lbrina tun dare, har kasa na durkusa na gaisheshi shi ya amsa da fara'arsa kuma yayimin godiya. Yana fita tace nazo muyi break, kunun gyada da plantain kawai na Iya ce, aunty Salma tace Aysha akwai abinda yake damunki, ko vakyason zama damu ne? Sbd dazu dana fito naga hawaye a idonki, nace wallahi ina son zama daku akwai kannena wanda ada nayi zaton uwarmu daya ubanmu daya, junior da basma kusan age mate din su nabil ne mu shaku sosai da yaran ni nake musu komai, duk lkcn dana tunasu sainayi kuka nakejin dadi. Eyya allah sarki kici gaba da hakuri insha Allah wata rana sai lbri, nace hakane kam. To me yasa kuma bakya son cin abinci? Nace ba kin ci nake ba, is my nature, dariya tayi tace aiko gashi nan bakya kiba,nima dariyar nayi daidai nan handsome ya shigo, yau kuma danyen boyel ne ajikinsa cream color gashin nan ya kwanta yayi luf muna hada idon na nemi nutsuwa ta na rasa sabd balain kyaun da yayi, karasowa yayi yace gud morning sis tace morning broz, nace masa INA kwana saida ya Dan lumshe ido ya bude sanan yayi murmushin da yake tafiya da imanin yan mata yace lpy kalau ya kwanan bakunta? Nima murmushin na mayar masa har saida kumatuna ya lotsa nace lpy kalau, duk abinda muke aunty Salma na kula damu, Amma saita yi kamar bamu take kallo ba. Ni nayi serving dinsa ya fara cin abincin saidai duk dagowar da mukayi sai mun hada ido, wani irin kallo yake min Wanda yasa wani mugun sonsa yake yawo acikin jinin jikina, har naji bazan Iya jurewa ba, mikewa nayi na koma daki na kwanta na fara tunani saura 2 month ayi bikinsa wasu zafafan hawaye suka fara zuba a idona, ina sonka kabeer, don Allah ka furta kace kana sona, at least ko baka aureni ba zanji sanyi a raina kuka nake sosai banji shigowarsa ba sai kamshin turaren sa daya daki hancina ya salm Aysha meya faru kuma? Don Allah ki fadamin Aysha, ko zaman gdn nan ne bakya so? Nace aa to fadamin don Allah meye matsalar ya karasa maganar cikin tsananin damuwa. A zuciyata nace ciwon sonka ne matsalata, Amma a fili sai nace ba komai iyayena na tuna bansani ba ko sunada rai ko sun mutu, daugoni yayi ya rungumeni a ajikinsa kiyi hakuri beauty kinji, asan is painful Amma addua zakici gaba dayi indai suna raye Allah yayi gaggawar bayyana su nace amin, hankii ya dauko a aljihunsa ya gogemin hawaye sanan ya kuramin ido da sexy eyes dinsa yayi magana da wata irin voice din da ban taba sanin yanada ita ba yace kayimin alkawari bazaki kara kuka ba, dakyar na Iya cewa na daina, sanan yace zanje mu karasa meeting da muke da Mr President ina ganin sai dare zan dawo idan da wani matsalar kiyimin text kinji? Nace to, kuma don Allah ki ware kuci gaba da hirarku da aunty Salma,  kada kai kawai nayi. Harya fara tyfy ya jiyo yace ko Dan smiling bazaki yimin ba? Wani lallausan murmushi nayi masa da har saida kumatuna ya lotsa, sanan yace thank you my sis ya fice ya barni da kewarsa da kuma kamshin turarensa

Maman Aysha
[9/27, 14:55] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
1⃣4⃣5⃣➖1⃣5⃣0⃣

Shakuwa ce me tsanani ta shiga tsakanina da aunty Salma, wadda har jinta nake kamar blood sister na, na sake da ita sosai har tsokanar juna muke, shima mijinta dake Dan harka ne harshi ake zama ayita hira.

Yauma kamar kullum bayan mun kammala dinner muna zaune anata hira har megdn khairat tayi bacci akan cinyata, nabl kuma INA koya masa h/work saiga adon gari ya shigo, bayan an gaisa yace kwantar da yarinyar nan ki zobomin abinci yunwa nakeji nace to, daki na kaita Sbd tunda nazo gdn tare muke kwana da ita, cusccus akayi wit vegetable soup Dana zuba yace kawomin nan, cin abinci akan carpet yafi dadi nace to yanaci anata hira, nabil yazo ya dameshi sai tsalle yake ajikinsa duk ya hanashi cin abincin ma, yace kai tashi kaje ka kwanta kona Zane ka, banda kiriniya ba abinda ka iya. Dariya aunty Salma tayi tace ai kai ya gado, Sbd ka bani wahala kana yaro,  nan ta shiga bamu lbri tace bana mantawa lkcn da muka zauna a London a makotanmu akwai wani yaro, sunanshi selvesta duk ya girmemu, gashi Dan lukuti idan ya kama mutun baya yi masa da wasa Sbd karfinshi super master ake ce masa ga brodana da tsokana kuma idan yayi tsokanar aka dakeshi sai mum tace dole saina fita na rama masa, duk lkcn daka tsokano shi gbn har faduwa yake,Dariya mukasa gabadaya, mijinta yace kai Ashe matsoraciya ce ke, tace wallahi Dan bakaga yaron bane. Adon gari ne yace au ni na manta ma Ashe wayoyina a kashe suke bari na kunna, aikuwa kamar jira suke yana kunnawa calls ya fara shigowa, kuma duk rabi yan matane wasu ya amsa, wasu yayi rejecting kuma don jaraba yana gama amsa wani kiran, wani yake shigowa. Mijin Aunty Salma ne yayi dariya yace ka zama business cenre duk suka kwashe da dariya banda ni da kishi ya cikamin zuciya, wani kiran ne ya kara shigowa da hanzari na dago na kalle shi sainaga yayi wani smiling ya furta zuby can Kasan makogaransa cikin wata sansanyar unique voice dinsa yake mata magana kanajin hirar tasu ta soyayya ce nan take naji kirjina ya cushe, kaina ya fara sarawa tsananin sonsa ya fara yawo acikin jinina, kawai sainaji bazan iya cigaba da zama a wajen ba mikewa nayi nace musu saida safe aunty Salma da tun lkcn da yanayina ya canja tana kula dani tace tun yanzu zaki kwanta? nace eh bacci nake ji to shikenan Allah ya tashemu lpy nace amin

 Gani yayi hirar tata bazata kare ba, yace kinga zuby I will call you back later, Ina wani important Abu ne, be jira abinda zatace ba kawai yayi switching off. Dariya babansu khairat yayi yace wato hirar da kuke is not an important issue ko? Anya karbuwar data samu guarantee ce kuwa? Murmushi kawai yayi, aunty Salma tace ai wanan brodan nawa sai a hankali, Amma inaji ajikina akwai yarinyar da zata karya alkadarinka kwanan, kuma you can't denied it. Wata shegiyar dariya yayi yace haba sis kin manta halina, ADON GARI ne fa, aini bana bari son wata ya shiga zuciyata ballatana har ya dameni, nidai zasu soni kuma har zuciyarsu ta nemi bugawa akaina, Amma ni ba wata wadda yarinya data isa na shiga wani hali akanta. Haka kace ko broz? Eh, to shikenan we shall see, mikewa yayi nizan tafi saida safe. Suka amsa da To Allah ya kaimu yace amin

Ni kuwa tunda na shiga daki nake kuka, wani irin son shine yake addabata wanan wane irin rayuwane? Na kamu da son mutumin da besan inayi ba tabbas ko shakka banyi, ciwon son adon gari shi zai zama ajalina, ita kam zuby Allah ya taimaketa tazo duniya a SAA, Sbd ko be aureta ba, zata iya bada tarihin yayi soyayya da ita, ya Allah ka ciremin son mutumin nan a zuciyata don na fuskanci mayaudari ne, yayi amfani da bewar da Allah yayi mishi ya koyamin sonshi, kuma yayi ignoring dina koda wasa yaki ya nuna yana sona, why me kabeer? Me yasa baka tausayi na, me yasa baka barni da bakin cikin rashin iyayena ba, kake kokarin kara jefa rayuwata acikin matsala, wata zuciyar ce tacemin karki zargi kabeer Aysha ki zargi kanki, Sbd shi besan ma kina sonshi ba, kinyi mistake da kika bari sonshi ya shigeki sabda ba yanda zaayi mutun me kudi, kyakkyawa Dan asali me tulin yan mata buhu buhu ya amince ya aureki, dole yar asali zai aura. Saida nayi kuka me isata, daga baya kuma wani wahalallen bacci ya daukeni.

Maman Aysha
[10/14, 9:53 PM] Chopy: [9/28, 11:59] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓

1⃣5⃣0⃣➖1⃣5⃣5⃣

Gobe ne ranar da kabeer yace zamu koma kano muna zaune muna hira da aunty Salma wajen 5pm, kawai saiga kabir ya shigo, da gudu yara sukayi hugging dinsa dake yana nuna musu so sosai, waje ya samu ya zauna yace kuje a shiryaku mu tafi yawo aunty Salma tace bazakaci abincin ba? Eh yau bana sha'awa, zan sami abinda zanci a rose flower sweet and bakery, nayi karaf nace ka bude a garin nan ne? Aunty Salma tace ai baki Sani ba? Aikuwa ya kamata kije, sabda idan kika shiga na garin nan saiki raina na kano, iya kudin shiga kawai 5000 ne, Ki shirya kuje mana, idan kin dawo zaki bani lbr nace to bari na canja dressing.

Wani hadadden filtex lace nasaka, zanen lemon green da orange color ne ajiki, amma orange din bashi da yawa, rose silk na daura orange nasa sarka da Dan kunne na stones suma orange color, 20k na sayesu, mayafi da shoe&bag ma orange zama nayi nai make up sosai a fuskata sanan na fita, takalmin danasa me tsini ne kos kos din takuna ne ya janyo hankalin su zuwa wajena nan take adon gari yayi mutuwar tsaye, bina yayi da wani irin mayattacen kallo da har naji kafata tana hardewa, da kyar na karasa wajen cikin sanyin murya nace na gama yace OK muje, sis sai mun dawo tace to. Shima saida ya biya kudi muka shiga, haka dokar wajen take, gaskiya kabeer ba karamin me kudi bane, domin kuwa rose flower sweet and bakery dinsa na abuja kadai ya isa ya rikeshi, wato fadar girman wajen ma bata lkc ne, ba abinda babu a wajen, akwai swimming pool, wajen wasan yara ya zuba haddadun motoci irin na wonder land, sai wajen lilo na yara daban, na manya ma daban, akwai wajen game din table tennis, basketball, suluka, volleyball dadai sauran su, akwai lafiyayyen garden da aka kawatashi da hadaddadun shuke shuke irin Wanda ko ranka ne a bace idan kaje wajen saika nemeshi ka rasa, sanan akwai restaurant duk wani kalar abinci ko snacks da abinsha akwai shi awajen, in fact idan kana cikin wajen saika manta a 9ja kake.

Tunda muka shiga wajen muke cin karo da  hadaddun yan mata da samari, kai har matan aure baa barsu ba duk Wanda ya kallemu saiyaji mun burgeshi Sbd kyau da kuma dacewar da mukayi, direct wajen wasan yara muka je aka sasu mota suna ta murna mota tana zagayawa dasu, wasu kujeru muka samu muka zauna, kawai saiga wasu yan mata guda biyu sunsha kyau sukayi mana sallama, sanan daya daga cikinsu ta dubi adon gari tace don Allah ka temakeni ka bani koda 1 minut ne na ganka, basarwa yayi kamar beji me tace ba, Mr kabeer don Allah ka taimaka min, cikin fushi yace wai bakiga tare nake da wife dina bane, ban yarda ba, ba matarka bace ai daurin auren babban mutun  Wanda yayi suna har a kasar waje irinka bazai boyu ba, da yanzu duniya ta Sani Kai musulmi ne kuma da Allah na hadaka, don Allah ka taimaka ka saurareni. Mikewa yayi suka koma gefe sanan ta fara masa bayani ni sunana juwaira Yusuf, dad dina ne minister of education, ranar da akayi bikin bude wajen nan na fara ganinka, kuma tun ranar na kamu da sonka saidai na rasa yanda zan hadu dakai sai yau. Kneel down tayi don Allah Mr kabeer ka taimaka ka aureni koda ata biyu ne Sbd wallahi INA tsananin sonka, naji Amma ki tashi, Sbd gbdaya idon mutane akanki yake ban damu ba kallona da mutane suke ba shine matsalata ba, ka amince da soyayya ta shine matsala ta, to naji tashi muyi magana, mikewa tayi ta zuba masa ido, kiyi hakuri don Allah idan nace zan aureki nayi miki karya, ban taba sha'awar mata biyu ba kuma insha Allah har abda bazanyi ba, kuma na Riga nayi dating matar da zan aura so INA yimiki fatan alkairi Allah ya baki Wanda ya fini, Tahowa yayi ya barta a wajen tana kuka yana zuwa yacemin taso mu tafi garden nace yaran fa? Daya daga cikin staff dinsa na wajen ya kira yace ya kula dasu khairat idan sun gaji ya rakosu guarding yace to

Wajen sabd shakatwarsa kadai ya tanade shi, sai yazo ake budewa ya gyara wajen sosai muna zuwa ya kwanta akan grass carpet ya lumshe ido, ya Dade a haka sanan ya ya bude a hankali ya kira sunana cikin damuwa yace Aysha me yasa yan mata suke bina? me yasa suke cewa suna sona? Akwai kyawawan samari masu kudi, masu class, wasu dunfini kudi ma Amma me yasa yan mata basa binsu Sani? Why me? Banaso nayi hurting din mutun, amma yan matan da suke sona sunsa dole inayi, what am I going to do? Aysha fadamin meye solution? Me zanyi su dena bina ba tare da na wulakantasu ba? Wallahi dani mace ne, da nikaf  zan ringa sawa,  cikin wata cool voice yayi magana Aysha fadamin me yakamata nayi? Nace kayi aure, idan sukaga kayi aure zasu Dan rege binka. To wa zan aura? Zuciyata har yanzu batasan zuby, na kasa son zuby Aysha, akwai mutumin daya da zuciyata takeso, saidai abune me wahala aurena da ita ya yuyu. Me yasa? Is a secret, tashi yayi ya zauna ya rike hannuna sanan ya kafeni da wani irin kallon daya saukar min da kasala yace ki tayani da addua Allah ya warware min matsala ta acikin ruwan sanyi, will you? Kai na daga masa Sbd gabadaya jikina ya mutu. Wani lallausan smiling yayi yace mrs Faisal, kuna waya kuwa? Nace eh ai na fada masa ma gobe zamu tafi, kai sorry wallahi na manta na fada miki an fasa tafyar gobe, Sbd me? Kinsan dad dinsu khairat yayi tfy ko? Eh, shine tace na taimaka na bar mata ke zuwa next WK saiki tafi, kai gobe zaka tafi kenan? Nan take naji gabana ya fadi, duk da nasaba da aunty Salma, Sbd shi nake jin dadin zaman garin, Ciwon sonsa zai wahalar dani kenan,,,,,,,,Tunanin Faisal kike ko? Kiyi hakuri ai kuna waya, sati dayan kamar yaune a wajen Allah, muje mu tafi naga magarba ta kawo kai

Maman Aysha
[9/29, 17:37] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓

1⃣5⃣5⃣➖1⃣6⃣0⃣

Ana kiran sallar magrib muka shiga gd KB yayi alwala ya tafi masallaci nima daki na shiga nayi alwala bayan mun idar da sallah muka fito  falo aka debo take away din da mukayi a rose flower sweet and bakery muka baje gabadayanmu mukaci, sanan aka fara hira, sai wajen 10pm Mr kabeer ya mike yayi mana sallama har yakai bakin kofa ya juyo yace lovely sis ba rakiya? Murmushi nayi nace muje na rakaka har bakin mota na rakashi saida yace bude motar ya shiga sanan yace ina fata sati dayan da aunty Salma ta kara miki be bata miki rai ba? Wata yar sansanyar dariya nayi ace ba damuwa 1 WK din kamar yau ne ai. To ya zakiyi da Faisal? Zaki iya coping da rashin ganin sa harna 2 wks? A zuciyata nace wanan mutumin Dan renin hankali ne, kodai ya gane na kamu da sonshi, shiyasa yake min haka? Amma a fili sai nace face dinsa kawai nayi missing, Amma ruhin mu yanan manne da juna, da har nake jin kamar muna tare. Yanayin sa ne ya canja, cikin shan mur yace min gud nyt.

Yanayin yanda ya shiga damuwar nima sainaji banji dadi ba, jiki ba kwari na shiga gdn aunty Salma tace ya tafi nace eh, to zauna muyi wata magna dake nace to da gaske ne kin dauke ni a matsayin blood sister ki? Nace eh, zanyi miki tambaya Amma don Allah Aysha karki boye min komai ki fadamin gaskyr abinda yake cikin zuciyrki nace to, a zaman da nayi daku na sati daya nan, na fahimci akwai soyayya me zafi tsakanin ki da broda saidai kunki Ku gaskanta hakan a junanku, Sbd haka inaso ki fadamin kina sonsa? Kuka na fara eh ina sonsa Amma kuma nasan yafi karfina, nayi kokarin hana zuciyata ta kamu da sonshi, but I fell, ina tsananin sonshi Amma ba yanda zaayi kabeer ya auri marar asali Irina,,,,,sauri tayi ta rufemin baki karki damu shima yana sonki, naga zallar sonki a kwayar idonsa, nafi kowa sanin halinsa Aysha, kuma inaso ki Sani a sanina bayan ni, kece mace ta farko da kabeer yake zama yayi hira da ita cikin sakin fuska, kice mace ta farko da kabeer ya fita outing da ita, sanan kece mace ta farko da Ya nunawa caring, wanan shi ya tabbatar min da cewa he is in Luv wit you, kuma kema kinyi deserving a so ki, kinada wasu qualities da sai an Tara mata dubu baa sami guda goma irinki ba, matsalar ki guda daya rashin sanin iyayenki, wanan kuma bazai hada aure ba indai yana sonki, mun barwa Allah, yafi mu sanin dalilin da yasa yayi haka. Idan ba zaki damu ba inaso ki ringa amsa wayar Faisal a gabn broda kinji? Nace to, zaki iya tafiya saida safe nace Allah ya kaimu

Washe gari

Sai wajen 9am na tashi na shirya break fast, yau kunun gyda da kosai nayi Sbd aunty Salma tanaso sanan na soya Irish da plantain na dafa ruwan tea komawa daki nayi nai wanka, nasa wata English gown peech color nayi fakin din gashina ya kwanta luf a gadon bayana, idan ka ganni saika ce swara ce, Sbd muna kama sosai, saidai ni dimple dina ya fito sosai.

Sai wajen 9:30 ya shigo gdn a dinning ya samemu muna cin abinci, shima yazo yayi joining dinmu ba karamin murna yayi ba daya samu kunu da kosai Sbd yanaso sosai kallona yayi yace kinji dadin ki Aysha, gaskiya Faisal ya more bakida kiwa irin ta yan matan zamanin nan Aunty Salma tayi dariya tace gaji da shi, wanan santi kawai kake wa mutane, sai yau Kasan bata da kiwa daka kwashi koko da kosai? Phone dina ce ta fara kuka, INA dauka cikin sansanyar murya nace hlo swit heart gud morning, morning my dear I hope kin fara shirin tahowa dai ko? Wallahi an fasa tafiyar sai next WK, what? Ke bakya tausayina ne? Baki damu ma da halin da nake ciki ba ko? Aysha ko kin daina sona ne? Kinsan da yadda nayi 1 WK din nan kuwa? Wallahi ina sonka swit heart, I miss you beyond your expectations, ba yanda zanyi ne shiyasa don Allah ka kara hakuri, iam begging pliss! Naji Amma gobe zan taho abj idan yaso ma taho tare, Kayi hakuri don Allah, me gidan yayi tfy, may b bazai kai 1 WK din ba ma, kuma yana dawowa zan taho, bakya so nazo? Inaso mana, banaso kabar wajen aikinka ne to shikenan zan duba na gani, alright, bye take care I miss you, I miss you too.

Cikin nishadi adon gari yake cin kosan, Amma ina fara waya da Faisal yaji ya fita a ransa Amma haka yaci gaba da cusawa, wani irin kishi ne ya addabi zuciyarsa da kyar ya samu yayi controlling Kansa, Amma dayake he is very smart duk kallon da aunty Salma ta kafeshi dashi bata gano wani abu a fuskarsa ba. Muna gama wayar aunty Salma tace Faisal ne ko? Nace eh, ko cewa yayi zai biyoki? Nace eh, to ai da kin kyaleshi yazo, yanada gaskiya fa Aysha, Allah ya taimake shi ya sami finan discission irin ki ai bazai yi da wasa ba, ai komai yayi akan ki be fadi ba bcos you deserve it, wani irin shu'umin murmushi yayi yace sister iam going, nan take naji gabana ya yanke ya fadi, na rasa abinda yake min dadi aunty Salma ce tace tun yanzu? I have a lot to do ko kinsan Mutanen da Suleiman PA ya bawa appointment din ganina sunfi mutun Dari, kuma nayi missing mum sosai I need to see her. Shikenan Allah ya kaika lpy yace amin, kafeni yayi da sexy eyes dinsa yace Mrs Faisal me zance masa idan naje? Tell him dat I really miss him, OK I will, na tafi sai munyi waya nace to Allah ya kiyaye

Maman Aysha
[10/14, 9:53 PM] Chopy: [10/1, 10:44] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓

1⃣6⃣0⃣➖1⃣6⃣5⃣

Yana sauka a Kano ya tarar da jerin motocinsa sun zo daukar sa, direct gdn mum dinsa ya wuce a Nasarawa GRA yana shiga yaje yayi hugging dinta yace I miss you mum, I miss you too my son, ya sister ka da yaran? Lpy kalau tace na gaisheki ina amsawa, iam feeling Hungary me kk dafa min? Favorite dinka nayi kuma da kaina nayi maka, oh thank you mum may god bless you wit Aljannar firdaus murmushin jin dadi tayi tace amin son. Dakin sa na gdn ya shiga yayi wanka Yasa wata yellow shirt da black jeans Sanan ya zauna yaci abincin, saidai wani Abu daya tsaya masa a rai shine test din girkin Aysha kawai yake son ci, wani irin missing dinta yake, kadan yaci abincin yaji ya fita akansa jinsa yake kamar wani marar lpy, kallon da mum take binsa dashi ne yasa ya waske ya fara wata irin faraa Wato mum har yanzu kina nan da girkinki me dadi, abincin yayi dadi sosai wallahi murmushi tayi irin na manya sanan tace ai kuma bakaci da yawa ba, ah naci da yawa mana kinga fa kadan na rage, to idan ka gama inaso muyi magana dakai, gabanshi ne ya fadi Amma saiya daure yace na gama, dama so nake na tambaye ka lkcn da kaje Kaduna ka gaisa da neehal kuwa? Aa ai bamu hadu ba ma, me yasa? Ai na fada maka duk yanda zakayi ka nemeta Ku gaisa, Wallahi nima naso hakan tafiyar data tasomin zuwa abj ne tasa bamu hadu ba, Amma ita ta ganka ai, Kaine baka ganta ba. Inaso ka Sani har yanzu hanklina be kwanta da zubaida ba, dandai kace ita kk so ne, Amma idan har zakabi umarni na nafiso ka auri neehal Sbd kyakyawar yarinya ce da saika hada yan mata dari baka samu guda daya kamarta ba, kuma gata yar manyan mutane, na Dade inaso naga mun hada jini da familyn Alhaji Abdullahi Idris makarfi, don Allah son kayi hakuri ka cikamin burina. Duk da sanyin A/c dayake dakin saida gumi ya jike shi jagab, zuciyarshi yaji tana bugawa duk duniya ba wacce yakeso yaga farin cikin ta irin mum, yana tsananin gudun bacin ranta ya zama dole kenan ya auri neehal, kallon mum yayi yace to amma mun kun binciketa sosai? Kinsan fa bazata rasa Wanda yake sonta ba, na tabatta zatayi kotanason wani bazata ki auran ka ba, Sbd ba matar da zata Dora ido akan ka bataji ta kamu da sonka ba iam proud of you my son murmushin yake yayi yace Allah ya zabar mana abinda yafi alkairi, Amma don Allah mum karki ma iyayenta zancen tukun, ba komai ne yake burge wasu matan ba, ki bari mu dedeta kanmu tukun, shikenan my son Allah yayi maka albarka yace amin, a gdn ta yau yayi niyar kwana Amma sai ya fasa yayi mata sallama ya tafi gd.

Yana zuwa gd wanka yayi ya kwanta akan gado, Amma Sam bacci yaki zuwa, fuskar Aysha kawai yake gani a idonsa, tabbas yana son Aysha so me tsanani, bazai iya tuna lkcn daya fara sonta ba, shidai kawai abinda ya Sani shine sonta ya Riga ya gama yi masa illa a kowanne bangare na jikinsa, be taba sanin ya so yake ba sai akanta, kuma bazai taba iya rayuwa ba tare da ita ba Aysha ce rsyuwarsa itace farin cikin sa, itace komai nashi yanzu ya zaiyi da mum? Ta Yaya zai fuskanci mum yace bayason neehal Aysha yake so? Ta Yaya zai tunkari mum ya fada mata yarinyar da yake so baa San asalinta ba? Tabbas idan taji lbrn ta bazata taba amince maka aurenta ba wata zuciyar ta bashi amsa, ba abinda yake son gani yanzu kamar aysha, yayi missing cuty face dinta, smiling dinta, wani irin kuka ne me karfi ya kwace masa haka ya zauna saida yayi me isarsa, muryarta kawai yake son ji, kawai sai ya dauki phone dinsa ya fara dialing......

Tunda ya tafi naji gabadaya garin yayi min zafi nayi kokarin na boye damuwa ta Amma na kasa har aunty Salma ta gane halin da nake ciki, yau ko hirar da muka saba munayi na kasa da wuri na koma daki na kwanta tunanin sa ya addabi zuciyata, wasu zafafan hawaye ne suka fara zarya a fuskata, daidai nan phone dina ta fara kara ina dauka yace me kike baiiyi bacci ba Aysha? A zuciyata nace Dan renin sense, shi meya hanashi baccin? Kamar yasan tunanin da nake sainaji yace harna fara bacci saina tuna na taho na barki a wani gari da baki saba sosai ba, sai nake ji kamar na  takura miki, kuma nayi wa Allah alkawari zan rike ki bisa amana, zan kula da farin cikin ki har zuwa ranar da zan aurar dake, wanan dalilin ne yasa nace bari na tabbatar da kina cikin farin ciki kafin na kwanta, kuma da alama you're not in d mood, nasan tunanin Faisal ne matsalar ki, so zanzo na tafi dake gobe Sbd bana so na karya alkawarin Dana daukar wa Allah akan zan baki farin ciki, be jira abinda zance ba ya kashe wayar. Wato badan yayi missing dina ya kirani ba? Meyasa baya sona? Meyasa har yanzu ya kasa ganewa iam in Luv wit him? Farin ciki ka Dade da rabani dashi Kabeer, tun ranar dana kamu da sonka na rasa farin cikina kuka ne me karfi yaci karfina dakyar na samu nayi bacci

Maman Aysha
[10/2, 12:53] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓

1⃣6⃣5⃣➖1⃣7⃣0⃣

Washe gari
Yau ya kama Saturday bamu tashi da wuri ba sai 9am da sauri na shiga kitchen na hada break fast muna gama ci naje na gyara dakina Dana aunty Salma, sanan nayiwa su khairat wanka nima wankan na shiga ina fitowa na shirya cikin wasu English wear's rigar pink ce tanada Dan tsayi, amma bata karasa gwiwa ba sai blue jeans kayan sun kamani sunyi min kyau sosai, kara taje kaina nayi na daure da band ya kwanta a gadon bayana, make up nayi sosai Sbd yau har janbaki nasa me karatu Baku ganni ba nayi kyau kamar a sace ni, idan ba magana nayi ba sai Ku rantse daga kasar India nake😀lol

Ina fitowa naga nabil da khairat sunata kokawa akan ball, rarrashinsu nayi nace suzo muje garden din gdn muyi ball, aikuwa suka biyoni da gudunsu iskace me dadi take kadawa dake lkcn damina ne, da gudu muka shiga garden din muka fara ball da muka gaji da ball din sai muka Fara wasan gudu duk Wanda ya kamani saina cillashi sama na cafe, saina kara zubawa a guje yaran iya karfinsu suke bina Amma sun kasa kamani Sbd gudu nake sosai.

Shigowarsa gdn kenan har yaje bakin kofar falo saiya jiyo hayaniyarsu a garden, kawai saiya nufi wajen rungume hannunsa kawai yayi ya zuba musu ido yana kallonsu fuskarsa dauke da wani smiling da shi kade ne yasan maanarshi zuciyarsa ce ta fara bugawa, ba abinda yakeso irin yajita ajikinsa, a hankali lebensa ya furta I Luv you Aysha.

Kafafuwa na naji sun gaji da gudun, na juya baya naga still suna bina sai kawai na fara Neman inda zan boye musu, ta bayan wasu dogayen Flowers na shiga, ina juyowa naci karo da wata bishiyar fulawa na tafi luuu zan fadi Sbd dama na gaji, lumshe idona nayi INA zuba ido na ganni a kasa, kawai sainaji ni a jikin Abu me taushi kamar auduga, kamshin turarensa ne ya farkar dani daga duniyar Dana shiga a hankali na bude idona muna hada ido ya sakar min wani lallausan smiling dinshi me tsada, bansan lkcn Dana mayar masa ba, kyakyawar fuskarsa na zubawa ido INA kallo, a zuciyata nace kana tambayar me yasa mata suke binka? Abinda suke bi ai ba boyayye bane kabeer, zallar kyaun da Allah yayi maka suke bi, tabbas kabeer kayi gaskiya da kace dakai mace ne da nikaf zaka ringa sawa bcos you are more than handsome kanada kyau kabeer, ya Allah ka mallakamin kabeer, Allah ka taimake ni kayimin wanan gatan, ADON GARI sunan ya dace dashi sosai tabass kabeer adon gari ne da kowacce mace zatayi burin ta mallake shi hawaye ne ya zubo a idona batare da nasan fitowarsa ba.....katse min tunani yayi da cewa ya salm aysha kuka kike? Ko kin bige ne? Nace aa to meyasaki kuka? Ohh sabd na rikeki ko? Iam sorry naga zaki fadi ne shiyasa, da sauri ya sake ni sanan ya zubamin sexy eyes dinsa yace kike fitowa ba dankwali ko? Kuma yanzu idan wani yazo ya ganki a haka fa? Cikin  shagwaba dani kaina bansan na iyaba nace wallahi dankalin ne nauyinsa nake ji, yaushe ka shigo garin? Zuwana kenan ko cikin gdn ban shiga ba dariya nayi me karamin kyau sanan nace eyya to mu karasa cikin gdn muna fitowa naga su nabil sai nemana suke da gudu sukazo suka rungume shi suna cewa oyoyo uncle, lkc guda muka shiga cikin gdn aunty Salma tana zaune a falo da mamaki ta kalle shi tace broda yaushe a gari? Ina fata dai lpy? Relax sis every thing is normal, kawai dai nazo na tafi da Aysha ne, abinka da yan uwan da suka shaku da juna, tana jin voice dinsa ta gane acikin damuwa yake maganar. Mikewa tayi ta kama hannunsa suka nufi bed room dinta

For correction or contributions 08067063932

Maman Aysha
[10/2, 20:17] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓

1⃣7⃣0⃣➖1⃣7⃣5⃣

A bakin gado ta zaunar dashi sanan ta dubeshi tace nasan ko waye kanina, mutun ne me dauriya da zurfin ciki, sanan baka da sa Abu arai, komai da sauki kake daukar sa, kuma na Sani baka iya karya ba kuma baka son meyinta, kallo daya nayi maka na gane kana cikin matsaneciyar damuwa zama tayi a kusa dashi ta dafa kamanarsa sanan tace pliss my broda tell me the truth me yake damunka? Yar gdn senator Abdullahin Idris makarfi mum take son auramin, kinfi kowa sanin yanda mum ta dauka ki Mutanen nan, batason yan uwanta kamar yadda take son Haj Asiya, ba abinda bazata iya yimin ba idan naki bin umarninta. Ni kuma zuciyata Aysha takeso, INA son Aysha so me tsanani, mutuwa zanyi idan ban auri Aysha ba sister, kuma kinsan abin is very complicated iam very sure koba case din neehal mum bazata taba bari na auri Aysha ba indai taji lbrnta, wani irin kuka ya fara me ban tausayi iam confuse sister, iam totally comfuse pliss help me wallahi bansan ya zanyi ba nidai abinda na Sani kawai shine aysha ce rayuwata inhar ban auri Aysha ba to zaku rasani. Itama kukan take tabbas Aysha tafi dacewa dakai akan kowacce mace a duniya, kuma nima INA goyon bayanka, kuma daidai ta shigo da maganar auran neehal ne, da zamu samu a janye wanan maganar da sai indai karfin mu ya kare wajen ganin tayi accepting din Aysha. Sbd haka kayi hakuri ka kwantar da hankalin ka, ka mika alamuranka a wajen Allah idan har aysha matar kace duk duniya ba Wanda ya isa ya hana, kadai yanzu kayi tunanin yanda zaka soke maganar neehal, zanyi insha Allah, nifa rabona da neehal dinma tun bata fi 8 yrs ba, idan muka hadu a hanya ma bazan ganeta ba, gaskiya nima na manta kamanin yarinyar. Shikenan zamuje mu tafi INA matukar alfahari da samun yar Uwa kamarki, Allah ya raya miki zuria'arki. Kiyi hakuri da dauke Ayshan da zanyi, wallahi na kasa jure rashin ta a kusa dani, tunda na koma na kasa baccin kirki, dariya tayi tace ai na dade da ganoka amma sai kayi disguising dinmu, shima dariya yayi sanan suka fito a tare.

A kitchen ya same ni na Dora lunch ya watsa min wani shu'umin kallo yace zuwa nayi na tafi dake, Sbd Faisal ya matsamin dole saina dawo mishi da matarsa, dariya nayi nace kuma kaga be fadamin ba, dama ai bazai fada miki ba, kuma nima bance ki fada masa ba. Juyowa nayi muka hada ido nayi dariya nace bazan fada ba, me like dafa mana ne? Favourite dinka nake dariya yayi da har saida fararen hakoransa suka fito sanan yace kinsan favorite dina ne? Nace eh mana, to meye? Pounded yam wit egusi soup dariya yayi sosai yace baki canka ba dambu ne favorite food dina, ohhh sorry kuma wallahi baba mero ta taba fadamin, shagwabe fuska nayi nace Amma zakaci wanan dima ai ko? Kai kawai ya daga min ya fice yana dariya. Cikin kankanin lkc nagama komai na jera a dining, duk inda nayi idonsa a kaina yake har muka zo cin abinci, nan ma ya kafeni da ido, sainaji duk na kasa sakewa Dan kadan naci abincin na mike na koma daki, shi kuwa zama yayi yaci ya koshi bayan ya gama ya biyoni har daki yace nazo mutafi, sai alokacin naji hankalina ya tashi Sbd mun saba da aunty Salma sosai har waje ta rakoni ta hadamin shatara na arziki muna zuwa bakin mota naga yanda jikin su yayi sanyi itada su nabil sainaji kamar kar na tafi, kawai saina Dora kaina a jikin motar na fara kuka, dama itama kadan take jira kawai saita karaso ta rungume ni tana kuka, folding din hanunsa yayi ya zuba mana ido yana kallon mu dayaga abin bana kare bane sai kawai ya janye aunty Salma ya maida ita gida, harya dawo INA kuka kama hannuna yayi yasani a mota driver shi ya bude masa ya shiga ya zauna a kusa dani, driver ya ja muka nufi airport.

Muna sauka a kano escort dinsa suka zo suka dauke mu, direct gdna muka wuce  muna shiga naga an gyara gdn banda kamshin turare ba abinda yake kallon sa nayi da niyar tambaya, kawai sainaga baba mero ta fito daga kitchen da gudu na tafi na rungume ta nace i miss you baba mero, sanan na durkusa na gaishe ta sanan nakai kayana daki na dawo kallona yayi yace nifa iam hungry ki taimaka ki dafamin light food zanje gd nayi wanka na dawo nace to, nima wankan nayi nasa wata English gown yellow sanan na shiga kitchen nayi masa potatos ball da lemon kankana da madara, na kara saka turaren wuta a gdn. Sanan na dauko wayata na kira aunty Salma mun Dade muna hira da ita sanan mukayi sallama.

Sai wajen 8 pm ya shigo gdn ni nayi serving dinsa yaci abincin banda santi ba abinda yake bayan ya gama muka fara hira, daidai nan Faisal ya kirani INA dauka yace yana waje, nan take gabana ya fadi sainaji bana son fita adon gari yana nan, Amma sai nace masa OK gani nan zuwa. Dagowa yayi yace INA zaki? Faisal ne yazo, dama kin fada mishi kin dawo ne? Eh ya kirani dazu, OK saiki tashi ki je ai, ya maida kallonsa kan phone dinsa, kasa tashi nayi saida ya kara cewa jiranki ake fa, sanan na tashi jiki ba kwari na fice,  muna zaune da Faisal yazo ya shiga motarsa ya fice daga gdn, Faisal yace yau me yasami Mr kabeer? Nace me ka gani? Naga ko yayi min magna, kamar be taba sanina ba, murmushin yake nayi nace may b sauri yake

Maman Aysha
[10/14, 9:53 PM] Chopy: [10/3, 12:40] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓

1⃣7⃣5⃣➖1⃣8⃣0⃣

Yana barin gdna gdnshi ya wuce zuciyarsa banda bugawa ba abinda take yakamata nayi saurin daukar mataki akan soyayya ta da Aysha, idan ba haka ba I will loose her phone dinsa ya dauka ya fara dialing no kamal, duka biyu ya dauka hlo adon gari garin? Lpy kalau ango, tunda amarya ta tare najiga shiru, fushi nake dakai Sbd bakazo kaga dakin amarya ba, kayi hakuri zanzo insha Allah, to Allah ya kawo ka amin, ya lbrn Mutanen gdn? Suna nan kalau, ya neehal ita yaushe ne bikin nata? Ankusa da yanzu tare aka hada ma, mijin da zata aura ne yayi tfy, Amma yanzu ya dawo, Allah sarki shima Dan Kaduna ne mijin? Eh Dr haidar ba, Dan abokin dad dinmu ne alhaji Bashir bakori, shima likita ne yanada asibiti me suna bakori obstetrics $maternity private Hosp, acan neehal take aiki, eyya Allah ya taimaka, Bari na barka haka saida safe to Allah ya kaimu nagode sosai.

Dr marwan friend dinsa ya kira, suna gaisawa yace marwan Kasan Dr haidar Bashir bakori a Kaduna? Sosai ma, he is my friend, don Allah tromin no sa don Allah, me zakayi da ita? Don Allah tromin koma meye zakaji daga baya, OK to zan tromaka yanzu

No tana shigowa ya fara dialing, ana dauka suka gaisa, sanan ya fara masa bayani kamar haka" sunana kabeer M BAGAUDA, mu family friends din gdnsu neehal ne, mahaifiyata tana kokarin hada aurena da neehal, ba tare da saninta ba, kuma nasan kai take so Sbd haka na kira na fada maka kayi saurin yin wani Abu akai, domin kuwa akwai kyakyawar fahimta a tsakanin parents dina da nata, idan har mum dina tayi magana to ba abinda zai hana a auramin ita, Sbd haka Sbd haka kayi kokarin yin wani Abu daga yanzu zuwa next WK, banaso na zama sanadin raba masoya masu tsananin son junansu irinku. Wata sansanyar ajiyar zuciya yayi sanan yace nagode Mr kabeer tabbas neehal ce rayuwata, kuma rabani da ita tamkar rabani da rayuwata ne, insha Allah tun daga yau zan fara daukar mataki, nagode Allah ya saka da alkairi

      3days later
Suna zaune da mum dinsa suna hira aka kirata a waya, tana dubawa taga Haj Asiya da sauri ta dauka bayan sun gaisa Haj Asiya tace dama kira nayi na fada miki gobe zaa kawo lefen yarki, kiyi hakuri don Allah na fada miki late, Wallahi abin ne ya taso urgent, muma be fada mana ba sai jiya. Jiki a mace mum tace oh ikon Allah dama kun mata miji ne? Eh anyi mata HAJIYA, ai Dan abokin abbansu ne ma, to Allah ya tabbatar da alkairi tace amin, amma sai kinzo ba HAJIYA tunda abin yazo a kurarren lkci, bikin nan da wata daya zaa saka, so in Allah ya kaimu bikin kyazo, to shikenan Allah ya kaimu.

Kallon shi tayi rai a bace kaji wai lefan neehal zaakai gobe, a zaune yake Amma saida ya mike, neehal din da kike so na aura? Eh wallahi, kai Amma wanan Abu be yimin dadi ba mum, naso na cika miki burinki, naso na auri neehal Sbd na faranta miki mum, Amma Allah yasa haka shi yafi alkairi tace amin son, kaima Allah yayi maka sauyi da mafi alkairi yace amin, bari naje gd amma zandawo da daddare insha Allah, to shikenan saika dawo.

Yana fita ya kira aunty Salma a waya ya fada mata duk abinda ya faru, tayi murna sosai sanan tace zan shigo kano gobe insha Allah, Sbd haka kafin nazo kayi kokari ka sanar da mom maganar Aysha, to shikenan sis nagode.

7:30pm
Ya shiga gdn mum cikin sa sanye da farar jallabiya saida ya durkusa ya gaisheta sanan ya zauna, sun Dade a zaune ba wanda yayi magna, sanan daga bisani ya daure yace mum wata magana nake so muyi dake, go ahead son INA jinka, dama game da zancen aurena ne, tunda Allah beyi da neehal ba, na samu wata yarinyar da nake so, alhamdulilla mum tace, Abu yayi dadi wacece ita? Yar gdn waye? Kuma a wane gari take? Mum ban taba yi miki karya ba, kuma yanzu ma bazan miki ba Amma don Allah mum inaso ki taimaki rayuwata ki amince min da auranta sabd ban taba son mace a duniya kamar yanda nake sonta ba. Sunanta Aysha, a gdn alhaji Ahamad TURAKI ta rayu tun tana jaririya, shi ya bata tarbiya ya bata ilimi daga karshe ya koreta Sbd son zuciya, ataikaice dai a yanzu batasan kowa nata ba, Amma idan kin amince min ni zan aureta haka, tanada tsananin kirki, tanada tarbiya, tanada kyawawan dabiu da kallo daya zakiyi mata kiji kina sonta.........wata mahaukaciyar tsawa ta daka mishi da har saida yayyan hanjinsa suka kada, sanan tace duk abinda take dashi ya tashi a banza tunda bata da asali, idan har kaga auran nan ya yuyu saidai akan Abu biyu, ko bana Raye, ko kuma bada yawuna  ba, Amma indai ina Raye ban amince ka auri yarinyar da bata da asali ba da kakkausar murya ta karasa maganar mikewa tayi zata shiga daki yayi sauri ya rike kafarta yana wani irin kuka me ban tausayi don Allah mum ki taimaka min, wallahi Aysha ce rayuwata, idan har ban aureta ba zan iya rasa rayuwata, wallahi mum idan ban aureta ba mutuwa zanyi plissssss! Aikuwa saidai ka mutu, daidai ka auromin Marat asali a yanda matsayin ka yake a Nigeria, gara ka mutu ta zare kafarta ta shigewarta daki. Ya Dade yana kuka a wajen, daga baya ya dauki key motarsa ya fice daga gdn

Maman Aysha
[10/3, 17:44] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓

A kwance nake abin duniya yayi min zafi, na rasa inda zansa kaina tunanin kabeer da sonsa ne fall zuciyata yau kwanansa uku kenan rabonsa da gidan nan, sanan idan na kirashi a waya baya dauka nayi duk tunanin da zanyi ko zan gano lefin da nayi mishi Amma ban gano komai ba, kullum acikin zuba ido nake ko zaizo amma shiru gashi yace na daina fita office. Baba mero tayimin rarrashin duniya amma na kasa hakuri.

Ina idar da sallar isha'i naji wani irin zazzabi ya rufe ni, kawai saina tafi daki na shiga bargo na kwanta banda rawar Dari ba abinda nake, ga wani irin missing din kabeer da nake, daidai lkcn ya shigo gdn a sukwane, ko gaishe da baba mero beyi ba yace ina Aysha? Tana daki, kawai sai yayi hanyar dakin a bakin gadon ya zauna kamshin turarensa sa ne ya tabbatar min shine da sauri na mike na zauna Aysha me yasameki kk kuka? Cikin shagwaba nace bakai bane yau kwana uku baka zo gdn nan ba, kuma na kiraka a waya kaki yin picking,  nayi maka text ba reply.  To Amma meya dameki da rashin zuwana? Ba Faisal yana zuwa ba? Kafe shi da ido nayi INA kallon kwayar idonsa, at d same time kuma hawaye yana ambaliya a idona, nayi miki tambaya kinyi shiru? Meyasa kika damu da rashin zuwana? Sbd INA sonka, ko kanaso ka fadamin har yanzu baka gane INA sonka ba? Meyasa baka tausayi na? Meyasa.......shitttt hannunsa ya Dora a saman pink lips dina Aysha nima INA sonki kuma INA tausayinki, ban taba sanin meye so ba sai akanki, Aysha you're my first Luv, my heart, my soul, my everything idan har ban aureki ba zan iya rasa rayuwata, kuma mum bazata taba bari na aureki ba dole sai an gano family ki, inaso ki kara tambayar su mum dinki ba wani leaked da zai baki Wanda zai taimaka wajen gano su? A iya bayanin da sukayi min gaskiya babu, Amma zan kirata ta Kara tambayar min shi, is alright ni zan tafi saida safe, hannuna ya rike inaso ki Sani INA sonki kuma duk duniya ba Wanda ya isa ya rabani dake gud nyt

Wani irin farin ciki ne ya kamani, nan take na nemi zazzabin da nake na rasa duk da akwai a lot of challenges a gbna Amma Kalmar so daya furta yana min tasa na manta da komai. Baba mero ce ta shigo dakin hankali a tashe me yace miki Aisha? Baba mero ki tayani murna, kabeer ya furta yana sona, ya amince da soyayya ta yau, dariyar farin ciki tayi tace alhamdulilla Allah ya tabbatar da alkairi nace amin, yanda naga dare haka naga rana Sbd farin ciki, a Daren na kira mum na tambayeta tace bata Sani ba, kuma tana tsoron yiwa dad magana sabda ya hanata tayi mishi mgn akan abinda ya shafe ni, sai nace ta a wacce police station ne? Tace ta tarauni ce, anan mukayi sallama tanata kuka tana yimin addua.

      Washe gari
11am a kano tayiwa aunty Salma, tana zuwa gdn mum ta wuce ta sameta tayi kuka idonta duk sun kumbura nunawa tayi kamar batasan abinda yake faruwa ba tace mum baki da lpy ne? Ai gara rashin lpy da abinda yake damuna, subahanalla me yake damunki? Dan uwanki ne yake son jefani acikin wani hali wai ya rasa wacece zai aura duk yan matan duniya sai marar asali. wanan ce damuwarki? Kwarai kuwa, to ki kwantar da hankalin ki wanan ai ba abin damuwa bane mum, bakisan me Allah ya rubuta akan abin ba, ni a ganina indai yarinyar mutuniyar kirki ce kawai ki barshi ya aureta mum.......rufe min baki daga ke har shi Baku da hankali, dama nasan bayan shi zaki bi,,,,,,,basu San shigowarsa ba muryar sa kawai sukaji yana cewa don Allah mum ki temaka min na aureta, sister don Allah kisa baki mum kar sai bayan na mutu kizo kina Dana Sani, Sbd wallahi idan baki bari na aureta ba mutuwa zanyi, ya karasa mgnr yana kuka, itama aunty Salma kukan take. Ka mutu mana wanan wacce irin tsinanniyar yarinya ce da take Neman wargazamin family na? Wanan ai ta zama annoba wai a INA ma kasanta? Ya zama dole tabar garin nan a yau, ko kuma nasa akasheta, bari na kira Dan lami akarada ya samomin address dinta, yanajin haka ya mike ya fice daga gdn

Direct gdn da nake ya nufu a hargitse yace ki sauri ki shirya duk wani Abunki me amfani, zanzo na daukeki mutafi BAGAUDA a daura mana aure, kuma ana daurwa zamu bar kasar Sbd haka ki sauri ki shirya Kai kawai na gyada masa ya fice daga gdn, yana fita na hada kayana na bawa baba mero 30k nace ta koma gd, sanan nasa hijabi da nekaf, na dauki key din mota baba mero tana kuka nima inayi na fice daga gdn.

Direct police station na tarauni naje nayi musu bayanin abinda ya kawoni, suka binciko file din sukace tabbas anan ne, saidai Wanda yayi handling case din a waccan lkcn yayi ritaya, nace to su taimaka min da address din gdnsa naje, sukace to, 10k na basu su raba nayi godiya na tafi.

Alhamdulilla na sami gdn mutumin a naibawa yake, kuma na sameshi yayi min bayani cewa matar tace a wani asibiti ta satoni me suna Dr Eze clinic $maternity a Zaria, unguwar chikaji, godiya nayi masa sosai na bashi 10k, sanan na dauki hanyar zariya

Maman Aysha
[10/14, 9:53 PM] Chopy: [10/4, 12:09] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
1⃣8⃣0⃣➖1⃣8⃣5⃣

Tafiyar 2 hours ne ya kaita zariya, da tambaya ta sami unguwar, tana shiga cikin unguwar ta tambayi asibitin aka nuna mata, saidai abinda ya firgitar da ita shine asibitin ya tsufa sosai daga gani an Dade baa bude shi ba, na Dade a bakin wajen a tsaye daga baya na hango wani dattijo da shekarunsa zaikai 55 yana zaune a kofar gdnsa, karasa wa wajensa nayi na durkusa na gaisheshi shi, sanan nace don Allah baba tambaya nake yace inajinki yan nan, ni yar jarida ce, nazo ne nayi tambayoyi akan asibitin can, kuma na ganshi a rufe, wai ai asibitin nan yakai shekara 19 da rufe wa, meyasa aka rufe shi baba? Sbd an sace wata jaririya a asibitin, to yanzu a INA zan samu me asibitin baba? Yarinya me asibitin nan tunda yayi ritaya ya koma jaharsu dama Dan anambara state ne. To don Allah zaka iya tuna iyayen yarinyar da aka sace? Kuma don Allah suna raye ko sun mutu? Yana nan a Raye, uban dakina ne sati uku daya wuce ma naje wajensa yatemakamin da kudin gado 1 million ya bani, mutun ne me tsananin kirki da temako, amma yafi shekara goma da komawa Kaduna, kuma akwai matakan tsaro sosai a gdn, domin kuwa be zama dole abarki ki shiga ba nima don securities din gdn sun sanni ne, sbd ni tsohon driver sa ne. cikin farin ciki nace baba nice jaririyar da aka sace don Allah ka taimaka min ka kaini gdnsa a Kaduna yanzu, nayi maka alkawari zan baka 500k  nima, aa yarinya ya zaayi ban sanki ba na yarda dake, yanda rayuwa nan ta koma, gaskiya bazan je ba, zan dai yi miki kwatance kije durkusa wa nayi nace don Allah baba ka taimaka min kaifa da bakinka kace akwai tsaro a gdn, idan naje ni kadai ba zaa barni na shiga ba wallahi ni ba macuciya bace, to shikenan idan dai har da gaske kk ke yarsa ce to tabbas yau kakata ta yanke saka domin kuwa a wancan zamanin ma million daya yasa duk Wanda ya samoki, Amma ba a sameki ba,  to Amma kinada abinda zaki nuna musu da zasu yarda cewa ke yarsu ce? Eh inada shi, to shikenan Allah ya kaimu lpy nace amin.

Cikin nutsuwa nake tuki na matsu mu karasa kd naga iyayena farin ciki ne fall zuciyata ji nake kamar a mafarki, wai yau nice naji wani Abu game da iyayena, wata zuciyar tace wani Abu kawai? Ai yau ranace da bazaki taba mantawa da ita a rayuwa ba, ni kadai nake dariya Sbd tsabar farin ciki

A kofar wani dankareren gd yace na faka motar, nace masa nan acce unguwa ce baba? Yace unguwar rimi kenan, nace kai Amma unguwar tanada kyau fita yayi yayiwa masu gadi magana batare da mata lkc ba muka shiga gdn. Gate uku muka tsallake kafin mu hango kofar falon shiga gdn, fadar haduwar gdn baa magana, a kofar falo muka tsaya ya kirashi a waya ya fada masa cewa yana tafe ne da wani abin alajabi da mamaki, abin mamaki na me kuma mallam musa? Yallabai kayi mana izini mu shigo zaka ga komeye, OK shigo, bude mana kofar akayi muka shiga muka zauna a falo few minutes sai gasu shida kyakyawar matarsa waje suka samu suka zauna, sanan yace inajinka mallam musa, wanan yarinyar ce ta sameni tayi min bayani cewa itace yarku da aka sace shekaru 19 daya wuce, a tare suka mike sanan matar tasa tace cire dikaf din fuskarkarki, ba musu na cire daidai nan neehal take sakkowa daga kan step muna hada ido tayi mutuwar tsaye cikin tashin hankali matar gdn tace tabbas ko shakka banyi ke yata ce, sabd dama Ku identical twins ne keda neehal, saida me zaki kara nuna min na tabbatar da hakan? Hand bag dina na bude na dauko zanin goyo, pink din overall da kuma yar karamar azurfar da mum ta bani na mika mata, a lkc guda suka zube sukayi sujjada a kasa, sanan suka furta alhamdulilla a tare, da gudu matar tazo ta rungumeni tabbas ke yata ce nawal, dama kina da rai, Allah mungode maka daka nuna min wanan rana, zuwa yayi ya janyeni daga jikinta ya zaunar dani akan cinyarsa ya rungume ni tsam ajikinsa da har inajin bugun zuciyarsa neehal ma da gudu tazo ta rungumeni kuka muke sosai ba Wanda yake bawa wani hakuri, mallam musa yana gefe yana kallon ikon Allah, saida mukayi me isarmu sanan kowa yayi shiru, sai alokacin ammi ta tuna ta kira Yaya kamal ta fada masa cikin murna da farin ciki yace yanzu zai biyo flight ya taho. Godiya sosai Abba yayi wa mallam musa sanan ya bashi kyautar 5 million murna wajen mallam musa baa magana daga karshe yayi mana sallama ya tafi

      8pm
Zaune muke akan dining muna cin abinci cikin farin ciki da nishadi har Yaya kamal da amaryarsa sun karaso, neehal ce ta kalli ammi tace dama mu yan biyu ne Amma Baku taba fada mana ba? Yaya kamal yace ni na Sani, kece dai baki Sani ba, tace Allah sarki Ashe inada yar Uwa ban Sani ba shiyasa INA yawan kama ammi a daki da kayan jarirai a hannu tana kuka, idan na tambayeta saitace min ba komai, ni kuma nayi zaton ko son haihuwa take, gabadaya akada dariya har Abba sanan ta kalli ammi tace wacece babba a tsakaninmu? Ammi ta cewa neehal kece babba neehal, ke kika fara shan iskar duniya sanan sai ita Abba ne ya rike kafadata yace hankalin mu ba karamin tashi yayi ba lkcn da aka sace ki, kuma ina ne tabbatar miki da cewa tun lkcn muka shiga kuncin rayuwa tun ranar da akace an haifa min Ku ban kara shiga farin cikin da yakai nayau ba, nasan agajiye kike kuje dakin yar uwarki Ku kwanta idan Allah ya kaimu gobe sai ki bamu lbrn abinda ya faru tun lkcn da aka sace ki zuwa yau nace to Abba, nayi musu sallama muka tafi. Tare muka shiga da neehal tanata tsokanata wai dole nace mata Yaya neehal Sbd ta rigani shan iskar duniya. Tunda nake bacci ban taba yin me dadi irin na yau ba

Maman Aysha grp INA fata munyi celebrating din farin cikina daku? 💃💃💃 hhhhhhhh

Maman Aysha
[10/4, 17:32] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
1⃣8⃣5⃣➖1⃣9⃣0⃣

A bangaran kabeer kuwa, yana fita daga gdn da nake gdnsa ya koma yayi wanka ya hada duk important decuments dinsa, ya shiga mota ya taho gdn a. Hmm me karatu zokaga adon gari mutumin da yake yawo da motoci sama da goma yau tashin hankali yasa yana yawo da guda daya, guda dayar ma shi yake driving da Kansa.

Yana zuwa gdn yaga ba kowa sai megadi daya tambayeshi yace bamufi 30mint da fita daga gdn ba, phone dinsa ya dauko ya fara dialing no ta Amma ya jita switch off, saiya kira baba mero itama tace  nace mata ta koma gd ni na tafi Neman iyayena, Amma ban fada mata inda na tafi ba, yana kashe wayar ya kira Faisal ko yasan inda na tafi? Shima yace tun dazo yake kiran layina be samu ba, elbash ya fado masa arai, yana kiransa shima yace rabonsa dani tun jiya da mukayi waya, ya kira aunty Salma ma ya tambaya ko mum tasa a daukeni, itama tace ba ita bace, zama yayi a cikin motar yana kuka kamar ransa zai fita haba Aysha don Allah meyasa baki gujeni ba sai lkcn da nake tsananin son kasancewa tare dake? Meyasa baki gujeni ba sai lkcn da sonki ya gama yi min illa ajikina? Why Aysha? Meyasa baki kirani nazo an daura mana aure ba kk tafi? Kuka sosai yakeyi daidai nan elbash ya kirashi hlo yallabai munyi waya da mum dinta yanzu tace ta kirata dazu tace mata ta tafi zariya, OK to nagode elbash, ko nazo mutafi zariya tare? A ka bari kawai ba matsala zan tafi ni kadai, duk yadda ake ciki zanyi maka waya, to shikenan Allah ya kaika lpy yace amin. Decoments dinsa daya debo a gd ya cire daga cikin motar ya shiga ya ajiye a dakina, sanan ya dawo ya shiga motar ya dau hanyar zariya.

Gudu yake kamar zai tashi sama zuciyarsa cike da tunani iri iri, driving yake Amma hankalinsa baya kan titin sosai, yaje daidai daka tsalle hannunsa ya kwace, yaje ya daki wata bishiya dagan be kara sanin inda Kansa yake ba, compliment card dinsa aka samu acikin motar sai suka sami no Sulaiman PA suka kirashi suka fada mishi inda abin ya faru, cikin tashin hankali yace gasu nan zuwa, da hanzari ya kira sadiq suka tafi da helicopter cikin kankanin lkc suka isa wajen kafin su karaso sun yiwa Dr marwan friend dinsa waya yace su hadu a orthopedic Hosp din Dr Abdul (asmaul Husna).

Likitoci hudu ne akansa suna bashi emergency care saida suka tabbatar ba matsala sanan suka kyaleshi, saida har yanzu he is unconscious, kuma ya sami fracture a hannunsa na hagu . saida komai ya lafa Sulaiman PA ya kira mum ya fada mata, cikin tashin hankalin da basu taba fuskanta a rayuwarsu ba suka taho asibitin ita da aunty Salma, tunda sukaje suke aikin kuka mum sai fadin maganganu take na nadama, ba yanda su Suleiman ba suyi da ita akan ta tafi gd su su kwana a wajensa ba amma fur mom taki, tace dole ita zata kwana haka suka hakura suka kyaleta.

Yanda sukaga dare haka sukaga safiya, duk bayan mintuna mum take leka kirjinsa taga ko yana numfashi, da safe ma dakyar ta yarda ta koma gd tayi wanka abinci kuwa ko zancen sa baayi kallo daya zakayi musu ita da aunty Salma ka gane suna cikin matsanaicin tashin hankl.

     Kaduna
Tun wajen karfe goma na safe gdn mu ya cika da yan Uwa da abokan arziki, masu zuwa yiwa su Abba murnar ganina, kowa ka gani fuskarsa dauke take da faraa duk wanda sukazo sai neehal da Yaya kamal sun fadamin sunansu da kuma dangantakarmu dasu, haka dai akayi ta introducing dina acikin family. Gashi dai acikin farin ciki nake, amma Kasan zuciyata fall yake da tunanin kabeer ko ya yayi da yazo ya samu bana nan? Ko a wane hali yake yanzu? Duk inda yake nasan yana cikin tashin hankli Sbd kabeer yana sona, to yanzu ya zanyi kenan?  ki kunna wayar ki ki fada masa kinga parents dinki, yess haka zaayi, da sauri na dauko na fara dialing... Amma sainaji akashe, wasu hawaye ne suka fara zuba a idona masu zafi, daidai nan neehal tazo tace naje ammi tana kirana.

Tun jiya da daddare ammi take Neman layin aminiyarta ta fada mata taga yarta data bata Amma baa dauka ba, sai yanzu ta kara trying kawai saitaji ta dauka da farin ciki mum tace Maman yara tun jiya nake Neman ki na fada miki Allah ya bayyana min nawal, amma shiru baki dauka ba lpy kuwa? Ba lpy Haj Asiya, kabeer ne yayi accident kin ganmu a asibiti har yanzu baisan inda Kansa yake ba, salatin da ammi tayi ne yasa gabadaya muka maida hankalinmu wajenta har Abba, Abba ne ya fara tambayar meya faru? Kabeer ne yayi accident yana asibiti unconsciousness....inajan ambaci kabeer naji zuciyata ta fara bugawa Abba ne ya katse min tunani da cewa ai sai mu shirya mu tafi zama be kama mu ba, amma Ku neehal da Aysha Ku zauna, tunda da baki a gdn idan yaso in zamu kara komawa sai aje daku, da sauri nayi karaf nace don Allah Abba aje damu yau din, yace to shikenan kuyi sauri Ku shirya, ana cikin haka Yaya kamal ma ya shigo yace yanzu wani friend dinsa yayi mishi waya ya fada mishi, bakaken Arabian gown mu kasa nida neehal wato me karatu kamar da muke da neehal tayi matukar baci, komanmu iri daya ne voice dinmu, dariyar mu, tsayinmu everything saidai kawai na Dan fita haske kadan, kuma ni inada dimple ita kuma bata dashi Amma duk da haka ba karamin me curiosity bane zai ganemu, su Kansu Abba da ammi rikide musu muke, a Prado din Abba muka tafi da motoci guda uku na escort dake Abba senator ne.

Bamusha wahalar gane asibitin ba, muna shiga cikin garin kano rayuwata ta baya ta fara dawomin allahu Akbar, Allah me yanda yaso wai yau nice nazo kano acikin gatana, a cikin kwana daya kacal Allah ya canja min rayuwata, yanzu duk rayuwar Dana debe lkc inayi ta zama tarihi dama ance duk me hakuri yana tare da Allah, alhamdulilla allah nagode maka.

Neehal  da Yaya kamal ne suka fara shiga dakin da aka kwantar dashi, cikin rashin Sani aunty Salma ta rungume ta tana cewa Aysha INA kika shiga? Ya akayi kk samu lbri? Mum dinsu ce ta katse ta da cewa ke Salma neehal ce fa wanan ina kika sami Aysha kum...bata karasa magna ba muka shigo tare da ammi, gabadaya su kamewa sukayi suna kallon ikon Allah idona yana kaiwa kan kabeer na tafi da gudu na rungume shi INA wani irin kuka me taba zuciya, kabeer don Allah karka tafi kabarni, wallahi idan ka mutu nima mutuwa zanyi...

Maman Aysha
[10/14, 9:53 PM] Chopy: [10/6, 17:51] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓kABEER🏓🏓

1⃣9⃣0⃣➖1⃣9⃣5⃣

Kuka nake sosai me ban tausayi, Abba ne yazo ya janyeni daga jikin kabeer ya rungumeni ajikinsa, cikin sanyin murya yace min dama kin sanshi ne? Kasa bashi amsa nayi sai aunty Salma ce tace eh Abba itace matar dayake so ya aura, kuma akan hanyar tafy neman ta ya hadu da wanan tsautsayin, mum dinsu kabeer ce tace ikon Allah lalle rashin Sani yafi dare duhu, Ashe aysha yarku ce? Na dauki tsanar duniya na Dora mata, hannunsa ya fara motsawa a hankali sanan ya bude idonsa, a hankali ya fara bin yan dakin da kallo 1 by 1, saidai ya kasa dauke idonsa daga kaina da kuma neehal, idan ya kalleta saiya juyo ya kalleni kuma ya kasa magna. A hankali ya furta ya Allah idan marfarki nake Allah ka farkar dani, karasa wa bakin gadon nayi nace ba mafarki kk kabeer, komai kake gani gaskiya ne Allah ya amsa adduarmu ya nuna min parents dina, wanan twins sis dina ce sunanta neehal a hankali ya furta dama ke blood sister kamal ce? Ya salm Allah me yadda yaso, kokarin mikewa yake Amma Sbd karyar da take hannunsa saiya kasa saida Yaya kamal ya temaka mishi, sanan ya zaunar dashi, Dr marwan da Yaya kamal ne suka taimaka mishi yayi wanka yayi brush sanan aka bashi abinci yaci, sanan mum tace su Abba su karasa gdnta suci abinci ba yanda basuyi dani na bisu ba Amma naki nace zan zauna a wajensa suje su dawo, haka suka dunguma suka nufi gdn mum nida Salma kawai suka bari a dakin, dagowa yayi yace aysha ke bakici abincin ba, nace na koshi kici ko kadan ne kinji, nace to hira muke cikin tsananin farin ciki da son juna

Su Abba basu dawo ba zai after 4, suna zuwa befi da 15 mint ba sukace mu tafi, nan take hnklina ya tashi na marairaice nace don Allah Abba Ku barni na zauna anan, idan an sallame shi saina koma gd wata dariya Abba yayi wadda na tabbata ta yake ce, kafin yayi magana mum dinsu kabeer ta rungume ni tace Aysha kiyi hakuri ki bisu Ku tafi kinji, suna tsananin bukatar kasancewa tare dake, ko kin mata sun dauki shekaru masu yawa suna kishiruwar rashin ki, sai jiya Allah ya bayyana ki baki wani zauna tare dasu sosai ba kuma kice zaki zauna anan? Ki kwantar da hankalin ki time to time saiki ringa zuwa kina dubashi kinji nace to. Fita sukayi gabadaya suka barni dagani sai shi a dakin, na karasa jikin gadon nace zan tafi Allah ya kara sauki yace amin harna fara tafiya ya riko hannuna na juyo a hankali muna hada ido ya sakarmin murmushin sa me tsada sanan yace iam going to miss you Aysha, I wish you  safe journey, I Luv you a hankali na furta I Luv you too INA kuka saida na tsaya na goge hawayen daya zubomin, sanan naje na sami su Abba a waje muka tafi

Maman Aysha
[10/6, 20:58] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
1⃣9⃣5⃣➖2⃣0⃣0⃣

Sai jikin magrif muka shiga kd muna zuwa gd kowa ya shiga yayi wanka mukayi salla, sanan muka taho dining mukaci abinci, bayan mun gama Abba yace na basu lbrn rayuwata na zauna na fara basu tunda ga farko har karshe ba Wanda beyi kuka ba acikin su, sun tausayamin sosai sanan Abba yace haka Allah yake jaraftar bawansa, in banda jarabawa ya zaayi ace kamar yata tana yawon Neman inda zata zauna, Allah yasa haka shine mafi alkairi a rayuwarki nace amin. Sanan na kalli su Abba nace Abba kuma kunji lbrn wacce ta sace ni, kuma me yasa ta saceni? Yace kwarai kuwa, me aikinmu ce ta sace ki wato abinda ya faru shine

      Some yrs back
Ni Dan asalin garin makarfi ne, mahaifina shine sarkin garin, kuma tsohon attajiri ne, bayan na gama karatun sec sai maihaifina ya turani Cairo nayi university, kuma anan na hadu da mahaifiyarku ita balarabiyar misra ce so familyn mum dinki gabadaya suna misra kanwarta jalila ce kawai anan 9ja ita Hutu tazo suka hadu da mijin. Bayan na auri amminku har an haifi kamal saina fada harkar siyasa na tsaya takarar chairman din garinmu, da temakon Allah da temakon ubangidana alhaji Mohd BAGAUDA na samu nayi nasara, Sbd kirki da kuma kyautatawa jamaa da muke, bayan munciye shekarunmu sai yan garin suka kara tsaidani, a lkcn kuma akwai abokin takarata alhaji tasi'u hankalinsa ba karamin tashi yayi ba, lkcn da ake rungutsumin siyasa zaayi zabe, daidai lkcn aka haifeku bazan iya fadin irin farin cikin da nayi ba a wanan ranar domin kuwa nurse din data yimin albishir din haihuwarku ma kyautar mota na bata. Alhaji tasi'u shine yasa a saceki Sbd bokansa ya fada masa cewa duk duniya ba abinda nakeso kamar Ku, kuma dole sai anyi sacrificing daya daga cikin Ku asirin zai yuyu, wanan dalilin ne yasa ya hada baki da Uwani me aikin mu ya bata 1million ta saci daya daga cikin ku. A gdn gonarsa na kura sukayi da ita zasu hadu, Dake Allah ba azzalimin bawansa bane akan hanyarsa ta zuwa kura daga zariya yayi accident, kuma yasa aka nemoni yayi min bayani da bakinsa ya nemi gafarata, washe gari Allah yayi mishi rasuwa. Tun daga lkcn muke Neman Uwani amma ba lbrnta har se yanzu da kikazo mana da lbrn ta rasu. Mun shiga tashin hankali marar misaltuwa a game da batan ki, kullum acikin addua muke Allah ya bayyana mana ke indai kina Raye, Sbd haka ba abinda zamu cewa Allah sai godiya. Jibi insha Allah zamu koma duba kabeer, idan munje zaki rakamu gdn mutumin daya rekeki muyi misu gdy nace to Allah ya kaimu yace amin, naga dare ya fara ya kamata muje mu kwanta ko? Mukace to, kowa ya mike Yaya kamal ma yayi sallama ya tafi gdnsa.

Dake angyaramin dakina INA zuwa na haye gado na kwanta saidai fur bacci yaki dauka na so da tausayi n adon gari ne a zuciyata, phone dina na dauko na fara dialing no Amma akashe, wani irin xugi da zafi zuciyata ta fara in har banji voice dinsa to confirm bazan iya bacci ba, to wa zankira ya hadani dashi? Aunty Salma zuciyata taban amsa, da sauri na fara dialing no ta bayan mun gaisa nace mata ya me jiki tace da sauki, Amma ni na dawo gd Dr marwan ne zai kwana a wajensa nace ayya to Allah ya sauwake saida safe. Yanzu ya zanyi kenan? Neehal ce ta shigo dakin da sauri tace my sis ga hydar zaku gaisa INA karba yace kanwarmu ya kk? Nace lpya kalau, haka dai yayi tamin surutu, daga karshe mukayi sallama na bata wayar yanayin yanda suke ta soyayyarsu a wayar sainaji hnkl ya kara tashi, kawai saina fashe da kuka da sauri neehal tayi sallama da haidar tazo ta rungume ni meya same ki kk kuka sis? Na rasa yanda zanyi nayi mgn da kabeer, kuma gashi bani da no Dr marwan, hydar yanada ita bari nasa ya tro mana, ba mata lkc ya tru ai kuwa da sauri na fara dialing yana dauka nace ya hadamu, cikin unique voice dinsa yace aysha bakiyi bacci ba? Ta Yaya kake tunanin zan iya bacci bayan phone dinka akashe take? Tunanin ka ya hanani bacci kabeer,  tausayin halin da kake ciki ya hanani sakat, ji nake kamar na cire ciwon ya dawo jikina, inasonka kabeer, INA maka son da ko kuda banaso ya tabaka, kuma gashi na jawo maka ciwo kana zamanka, duk ni na saka a halin da kake ciki yanzu don Allah kayi hakuri kuka ya kwacemin, da wata irin cool voice yake magna stop crying Aysha, don't blame your self bake kika jamin ba haka Allah ya rubuta, kinga iam not feeling fine, kuma kukan ki yana kara tayar min da hankali so don Allah kiyi shiru, yanzu lkcn farin ciki ne, kinga yanzu ba abinda zai hana muyi aure ko? Nace eh, so dariya da godewa Allah ya kamata kiyi ba kuka ba kinji? Nace to, nayi missing dinki sosai yaushe zaki dawo ki ganni? Abba yace jibi zamu zo, Amma idan nazo bazan tafi ba, ni zanci gaba da kula dakai har saika warke, wata sansanyar dariya yayi yace are you sure? Nace yes, still dariyar yake da gaske zaki iya rikeni, ki feeding dina, kimin every thing da nake bukata, nima dariya nayi nace emana, yace to shikenan we shall see, I love you Aysha, nace I Luv you too, gud night OK night

Maman Aysha


[10/14, 10:22 PM] Chopy: [10/8, 18:50] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
2⃣0⃣0⃣➖2⃣0⃣5⃣

Washe gari a makarfi muka wuni aka zaga dani gidajen yan Uwa alhaji kakanmu kamar ya cinye ni sabd murna kowa sai Jana yake ajiki a hanya nake cewa dad dama haka muke da dangi? Yace su yanzu yan Uwana kawai kk gani, zamu sa rana muje misra kiga familyn amminku nace to Allah kaimu yace amin.

Sai wajen 6pm muka shiga kd, muna zuwa muka watsa ruwa mukayi sallar magrib, sanan nabi lfyr gado na kwanta bansan lkcn da bacci ya dauke ni ba, sai can naji neehal tana cemin na tashi muje muci abinci, nace nifa ba kullum nake cin dinner ba kuje kuci kawai ni zansha cooker Oates da snacks, wato bakya son cin abinci ko? Zan hadaki da ammi ai, da gudu ta fita dining tana zuwa ta tarar su kadai ake jira, ammi tace INA Ayshan kuma? Wai bazataci ba, cooker Oates zata sha Abba yace kirata, a waya ta kirani nazo Abba yace dole sainaci abinci nace Allah Abba nakoshi, Abba yace to je ki hada Oates din kisha nace to.

Ina daki INA duba abu acikin laptop dina saiga neehal ta shigo cikin shirin ta tace my sis hydar ne yazo, Amma ke zaki fara fita a matsayin nice, so nake na gwadashi na gani ko zai ganeki, amma fa sai kin cire kunyar nan taki, nasan zaki iya tashi ki shirya nace to, pyjamas ne ajikina Riga da wando kawai saina Dora bakar after dress akai ta bani turenta nasa, sanan tace swit man nake ce masa, kuma INA Dan durkusa wa idan zan gaisheshi nace to. Wit confidence na tafi INA zuwa bakin kofar naji gabana ya fadi, Amma kawai saina basar na shiga nayi mishi sallama ya amsa sanan na durkusa na gaisheshi na samu waje na zauna juyowa yayi ya kalleni yace nayi missing dinki sosai my baby, tunda sis dinmu ta dawo kin manta dani cikin shagwaba nace to ba muna waya ba, eh munayi, amma ba kamar eye contact ba, to ai yanzu gashi ka ganni ko? Murmushi yayi yace eh, kinsan INA sonki da yawa shiyasa, nafiso kullum na saki a gabana INA kallon ki, neehal ce ta shigo da tray ta durkusa ta gaisheshi nan take ya zama comfuse, zuba mana ido yayi yana so ya gane wani Abu kawai saina katse shi da cewa to ga kanwar tamu nan saidai ka manta baka tambayeta me jiki ba, Kasan fiancée dinta mukaje dubawa a kn jiya, may b zakasanshi ma Mr kabeer M BAGAUDA, yes nasan shi very nice guy, bansan shine patient din ba ai da naje na dubashi, wallahi baby guy din yanada kirki sosai wani farin ciki naji ya kamani, shaf na manta plan din da muka hada nace saika zauna dashi ma zakaji ya kara burgeka, shiyasa nake kara sonshi wallahi....... Cikin kidima da tashin hankali hydar yace kaddai maganar daya kirani kwanakin baya ya fadamin ta tabbata? Neehal a gabana kk cewa kina son wani?mikewa nayi nace relax Mr hydar, iam aysha tunda ka kasa ganemu ga neehal din can, sis iam sorry kinsan indai zaayi maganar kabeer dole sainayi magana, amma wacce magna kabeer ya fada maka hydar? Da mum dinshi taso hada auran shi da neehal, shine ya kirani ya fadamin Sbd na dauki mataki, juyawa yayi ya kalli neehal yace baby abinda yasa nace zan kawo lefe urgent kenan, turo baki tayi tace ni nayi fushi dakai tunda ka kasa gane ni, ta juya ta fara tafiya mikewa yayi da sauri yayi hugging dinta yace iam sorry my dear kamar taku ce tayi yawa sanan ya kalleni yace kanwarmu nice to met you, dariya nayi nace nice to meet you too, na fita na basu waje.

Da kyar ya samu ta hakura sukaci gaba da hirar su ta soyayya bayan ya tafi ta shigo dakina aikuwa na fara tsokanar ta hydar ya kasa ganeta a tsakanin mu, tace kaddai ki cika baki gb zamu je kanon ai ki bari idan kabeer ya ganeki saiki ji dadin tsokana ta, nace to shikenan Allah ya kaimu gben tace amin, hugging dina tayi tace gud night sis

Maman Aysha
[10/8, 21:33] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓
2⃣0⃣5⃣➖2⃣1⃣0⃣

Washe gari muna gama break fast muka fara shirin tafiya kano har dakin Ammi naje nace don Allah ammi ki rokar min Abba ya barni na zauna idan munje na karasa mgnr a kunyace dariya mum tayi tace to Mrs kabeer zan fada mishi Amma kinsan zamuyi missing dinki ko? Saidai muyi hakuri kawai Sbd mu faranta miki, nace thank you mum, you're well come my dota.

Wani hadaddan material muka sa me combination din yellow and red, dinkin Riga da siket ne kayan sun mana kyau sosai red rose silk muka daura, komai iri daya mukasa tunda muka fito falo ammi da Abba suka fara wani irin smiling na farin ciki, Abba ne yace you looks so beautiful my twins Allah ya raya min Ku mukace amin Abba, sanan yace Aysha kince zaki zauna acan ko nace eh yace to shikenan ba matsala muje ko, a tare muka fita a Lexus din Abba muka tafi da motocin escort dinsa guda uku daya a gaba, biyu a baya.

Asibitin muka fara zuwa, muna fitowa daga mota su mum dinshi suna shigowa sai su abba suka tsaya su shiga tare, kuma mukayi gaba, neehal tace ni zan fara shiga, kuma ni zanje a matsayin ki nace to, a zaune yake yayi daidai akan Gado da laptop a gabanshi, sanye yake cikin wata red shirt armless sbd hannunsa, da blue jeans ya kara kyau yayi fresh kamar ba jinya yake ba, shida sulaiman PA ne kawai a dakin, muna shiga neehal ta wuce bakin gadon direct, taja kujera ta zauna a kusa dashi sanan ta  gaisheshi ya amsa yana wani Dan iskan smiling, tace honey ya jikin yace da sauki daidai nan ya jiyo muka hada ido nace kanina INA wuni? Yana wata yar iskar dariya yace don't take me as a fool Aysha, kina ganin zaki iya bace min? Tun shigowarku na gane ki, wata sansanyar dariyar farin ciki nayi nace shiyasa nake kara sonka you're very smart, karasawa bakin gadon nayi nace Mrs hydar saiki tashi ki bani kujerar na zauna tunda ya ganeki INA wata yar iskar dariya,  tana tru baki ta mike ni kuma sai tsokanar ta nake, na kalli kabeer nace Yaya hydar kasa ganemu yayi, neehal tayi caraf tace ai sabd dare ne shiyasa, nace ba wani nan kareshi kawai kike muka yi dariya gabadaya, Abba ne suka shigo a tare sukace dariyar me kuke tayi ne haka? Na basu lbrn abinda ya faru suma sukayi ta dariya sukace ya kamata kiyiwa hydar abinda zai ringa ganeki da sauri neehal. Bayan sungaida kabeer Abba yace muje gdn naku Aysha nace to, gabadaya muka tafi har mum dinsu kabeer dama tun jiya na fadawa mum zuwanmu.

Muna shiga compound din rayuwar gdn gabadaya ta dawo min, INA gaba suna bina a baya muka shiga har part din mum, INA shiga su junior suka taho da gudu zasu rungumeni, da suka ga neehal kuma sai suka tsaya suna kallonmu, suka rasa wajen wa zasu acikinmu cikin tsananin farin ciki mum ta tare mu saidai itama tsayawa tayi tana kallonmu, ta kasa gane ni aciki ina ganin haka naje na rungumeta kawai saina fashe da kuka, sanan tace su ammi su zauna taje ta kira dad ya fita shigo dasu Abba da Yaya kamal, sanan yaje ya kira mama dasu Yaya zee duk aka hadu, bayan angama gaisawa abbanmu yayi bayani cikin nutsuwa, sanan yayi wa dad godiya sosai kuma yayi mishi addua domin acewarsa bashida abin da zai saka mishi, shima dad ya rokeni gafara yace wallahi besan ya akayi yaji tsanata da rashin tausayi na a zuciyarsa ba, Amma wallahi yayi nadama daga baya, mamace tayi caraf tace nima don Allah ku yafe min, nice silar komai Sbd ni nayi asiri na rabaku Amma wallahi nayi nadama Sbd tun yanzu ga sakamako Nagani da muna gani kamar mu kadai ne gatanki, Ashe babanki babban mutun ne a 9ja, don Allah ki yafemin kinji nace bakomai Allah ya yafe mana gabadaya. A gdn mukaci abinci sanan muka kuma asibiti harsu mum da dad, daganan su Abba sukayi sallama suka dau hanya

Maman Aysha
[10/14, 10:22 PM] Chopy: [10/9, 12:39] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓

2⃣1⃣0⃣➖2⃣1⃣5⃣

Su Abba suna tfy mum da dad ma sukace zasu tafi sun bar min su junior dake a gdn zan kwana tace idan na gama zata tro azo a daukemu nace to, suna tfy saiga elbash da murna na tareshi muka shiga ciki ya dubashi ya kara yimin murnar ganin iyayena, sanan yace motata tana nan zai mayar da batir din yakai a wanketa ya kawo min gobe nace to nagode, saida na rakashi har bakin mota sanan na koma. Haka muka zauna da aunty Salma da mum wadda yanzu take nunamin tsananin so, munata hira Sbd yanzu jikin nashi da sauki any time zaa iya sallamar shi ana kiran idar da sallar magrib su mum da aunty Salma sukace zasu tafi, kuma nasan Sbd sunaso subarmu musake ne, amma wani lkcn suna kaiwa 11pm basu tafi ba. Saida na rakasu har bakin mota sanan mukayi sallama na juya na fara tfy kenan kamar daga sama naji muryar Faisal yana kirana, tsayawa nayi har ya karaso ya kalleni yace kin kyauta Aysha, kin samu parents dinki Amma ko ki fadamin, yau kusan 1 WK kenan ba lbrnki yanzu ma Dr marwan ne yake fadamin adon gari yayi accident, kuma yace kema kina nan. Ashe dama soyayya kuke da adon gari? Kunya ce ta kamani gabadaya na kasa bashi amsa, any way ba matsala INA sonki, ban taba son wata ya mace a duniya kmr yadda nake sonki ba Amma inhar zanyi miki adalci, ya zama dole nayi hakuri ki auri abinda zuyarki take so, Allah yasa haka shi yafi alkairi a hankali nace amin nagode Faisal Allah yayi maka sauyi da wacce tafini, wani smiling yayi yace samun irinki da wahala Aysha, na Riga nayi loosing mu karasa ciki na dubashi ko? Nace to a tare muka shiga har cikin dakin muna hada ido dashi yasha kunu, Faisal ne ya karasa har bakin gadon yayi masa sannu ya amsa da fara'arsa har saida suka taba hira ma sanan na rakashi ya tafi. Kabeer yaji haushin rakashi Faisal din da nayi, Amma sai ya basar mukaci gaba da hira ban bar asibitin ba sai wajen 10pm dakyar na tafi sabda banaso nayi missing din shi su junior har sunyi bacci sai daukar su akayi, lkcn da muka karasa gd mum da dad suna zaune suna hira nima na zauna mukaci gaba da hirar sai wajen 11 muka kwanta.

Washe gari da wuri na tashi nai break fast nayi wanka, sanan nayiwa kabeer kunun gyada da kosai Sbd yace shi yake so, sai kuma nayi masa paper soup din kifi ragon ruwa soyayyen irish da kuma plaintai, nayiwa mum sallama dad ya bani key din motarsa camry 2015 na tafi da ita asibiti INA zuwa na samu har yayi wanka ya shirya an gyare dakin banda kamshi ba abinda yake akusa dashi na zauna nace gud morning my soul, yace morning beauty ya gajiya? Murmushi kawai nayi nace me zanyi serving dinka? Yace kunu da kosai INA budewa kamshin ya doki hancinsa, ni nake bashi a baki harya koshi sanan na zuba masa kifin ma na bashi saida na tabbata ya koshi sanan na debe kayan na sasu a gefe naje na wanke hannuna sanan na dawo mukaci gaba da hira, daidai nan Dr Abdul da marwan suka shigo Dr Abdul yace ai sallamarka ma zamuyi sai kawai aci gaba da treating dinka a gd yace to shikenan nagode sosai doctor yace a ba wani Abu, Husna tana tambayar ka idan ka warke ya kamata ka kawo mana madan su gaisa yace ba matsala zan kawota insha Allah awaya na kira su mum nace karsu zo an sallame shi zamu taho yanzu. Ni na rikeshi mukaje har mota, bayan ya zauna na zagaya na shiga su Sulaiman suna binmu a baya muka nufi gdn mum dinsu, a part dinsa na gdn zai zauna an tanadar masa duk wani abu na jin dadi daka sani munyi waya dasu Abba na fada musu ansallameshi, Abba yace neehal da hydar zasu zo gobe sauki shirya ki biyosu nace don Allah Abba kayi hakuri ko sati daya nayi, be gama warkewa ba fa dariya Abba yayi yace kai aysha na fuskanci kinfi son kabeer damu, wai ke bakisan munyi missing dinki bane? Dauriya kawai fa muke nanda lkc kadan nasan Kabeer zaice zai turo, so kinga bamu wani zauna dake sosai ba zaayi auren ki, nace to shikenan Abba Allah ya kaimu goben yace amin. Yauma sai dare na koma gd.

Maman Aysha
[10/9, 14:55] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓

2⃣1⃣5⃣➖2⃣2⃣0⃣

Yauma da wuri naje gdn, dasu basma mukaje ga yayyan aunty Salma khairat da nabil suka hadu sunata wasa, wajen 12pm su neehal suka karaso ita da hydar muka zauna ake ta chapter a dakin, saika manta ma zaman jinya muke sabd hanun yayi sauki sosai nida aunty Salma muka shiga kitchen muka shirya abinci me rai da motsi kowa yaci ya koshi, sanan mukaje gdn elbash nida neehal matarsa ta haihu mukayi musu barka ta you and your babys dream muka bi nasayi kayan baby na 20k, ita kuma aunty rahama na sai mata turmin Hilton da murna sosai ta tare mu, itama tayi mamakin kamar da muke da neehal mun Dade muna hira ta rokeni gafara nace na yafe mata, elbash ba karamin murna yayi ba, mukayi musu sallama muka koma gdn su kabeer Bayan munyi sallar laasar su neehal sukace zasu tafi nan take gabana ya fadi Sbd Abba yace na bisu, kirnta gefe nayi nace Abba fa yace na biku dariya tayi tace Mr Luv ammi tace a kyaleki, idan sunzo saiku tafi wato son kabeer ya rufe miki ido ko missing dina ma bakya yi ko? Wallahi ba haka bane sis...dadai nan mukazo bakin kofar falon waje, wata pritty girl muka gani tana ta hada su sulaiman da allah akan su barta ta shiga ta duba adon gari amma sunki, neehal ta kalleni tace  my sis akwai aiki a gabanki don gaskiya wanan kabeer din naki saikin kara daura belt, kinsan he is more than handsome, dole yan mata su bishi, ammafa bance kije kiyita damun kanki ba sbd yana sonki sosai. Mu muntafi sai munyi waya, nace to Allah ya kiyaye INA daga mata hanu muna dariya har suka bace, sanan na koma ciki.

5pm yahuza suya

Yan mata da samari ne zaune anata shakatawa kowa yana harkar gabansa, a gefe grp din yanmata ne masu ji da Kansu da yawan su zai kai su goma suna shan ice cream suna hira kawai saiga wata kyakyawar yarinya tazo wajen tace hii friends sukace hlo ralma ya gari tace gari ba dadi, kamar ya ba dadi?  Baku da labrn ADON GARIN yan mata da samari yayi accident a tare sukace what! Yaushe kenan? Cikin damuwa tace yau kwana hudu har an sallameshi ya koma gd, tab aini   banji lbrnsa ba kwana biyu I tot yayi tafiya ne, ya salam ya zama dole naje Dubiya koda bazai amsamin ba, kinsan ganin fuskar guy din nan kadai farin ciki yake sani koda kuwa hararata yayi, ramla tace aikuwa dakyar idan zaa bari ki ganshi, domin kuwa PA da body guards dinsa ne a gdn sai sunga dama ake shiga nima yanzu daga can nake da renin hankali littafi da Biro suka bani sukace na rubuta sunana. Zuby dake gefe tana sauraransu tun lkcn da akace yayi accident tayi mutuwar zaune a zuciyatta tace yanzu adon gari yayi accident har ya kwanta a asibiti Amma ban sani ba, cikin tashin hankali tacewa body guards dinta kuzo mutafi, tana tafiya suna take mata baya suka nufi gdn mum.

Su neehal suna tfy na bude motar da nazo da ita na dauko wata rigata aciki, na shiga dakin aunty Salma na gdn nayi wanka na dauki  rigar ta Dana dauko a mota English gown orange me spagetti hand ta Dan tsuke daga sama rigar tayimin kyau sosai na yane kaina da karamin orange gyale sanan na fesa turare a falo na sami mum da aunty Salma suna hira nayi musu sannu na wuce dakinsa, a zaune yake da friends dinsa harda Dr Abdul sunata hira, INA shiga na juyu da baya da sauri mikewa yayi ya biyo bayana, a corridor muka hadu yace ya kk koma? Kafin nayi mgn yace inason shan fruit salad nace to, saida na fadawa mum a kunyace sanan na nufi kitchen na fara hada mishi in few minutes na gama lkcn Dana kaimasa shida sadik ne kawai a dakin, INA shiga sadik ya fita a kusa dashi na zauna na fara bashi kamar wani karamin yaro yana sha muna hirar mu ta soyayya

Kamar an jefota daga sama ta shigo dakin suna hada ido ta fashe da kuka haba kabeer don Allah, wacce irin kiyayya kake nunamin? Ina matsayin matar da zaka aura, Amma kayi accident harka kwanta a asibiti ban sani ba. Kiyi hakuri zuby, wallahi hnklna ne baya jikina, komawa tayi ta daya gefenshi ta zauna sanan cikin kissa tace ya jikin? Yace da sauki dauke fruit salad bowl din tayi tace bari nima na samu ladan kawai ta fisge spoon din hannuna ta fara bashi abin mamaki sainaga ya bude baki yana karba, na kafeshi da ido amma ko ajikinsa nan take naji zuciyata ta fara zugi mikewa nayi zan fice daga dakin sainaji ya ruko hannuna yace INA zaki? Murmushin karfin hali nayi nace zan Dan Baku waje ne Ku Diskanta kaida madan dinka na zare hannuna na fice daga dakin

Maman Aysha




[10/14, 18:45] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓

2⃣2⃣0⃣➖2⃣2⃣5⃣

Ina fita daga dakin yace ta daina bashi fruit salad din haka ya ishe shi, bayan ta ajiye bowl din tace honey dama inason mgn dakai, ba tare daya kalleta ba yace inajin ki, yauwa Kasan a yadda muka yanke date din bikin mu nida kai, yau saura sati uku kenan bikin, kuma Kasan har yanzu a family Ku ba Wanda yaje gdnmu akayi mgn, ni kuma gsky banaso na rasaka, shine nace me zai hana tunda baka da lpy idan time din yayi a daura auran idan yaso daga baya sai a daura auranku da Aysha kuma a hada bikin lkc daya ayi, murmushi yayi sanan yace duk yanda kk ce haka zaayi Allah ya kaimu lkcn cikin kissa da farin cikin samun nasara tace amin

Ni kuwa INA fita daga dakin wasu hawaye suka cika min ido, saida na tsaya a corridor na goge sanan na fita falon, aunty Salma da mom suna zaune na musu sannu na wuce daki, aunty Salma ce ta biyoni tace aysha me yake faruwa naga kmr ranki a bace yace? Kakaro murmushi nayi nace kaina ne yake ciwo shine nake so na Dan kwanta tace OK bari na baki pcm kisha Allah ya sauwake nace amin

Tana fita na shiga tunani wato kabeer har yanzu yana son zuby? Anya da gaske yana sona kuwa? Wata zuciyar tace INA ganin tausayin ki kawai yake, amma gaskiya yafi son zuby. Wani kishi naji ya addabi zuciyata kawai saina dauki phone dina na fara kiran neehal, bugu daya ta dauka INA kuka na bata lbrn abinda ya faru, nace kuma da yacemin baya sonta fa, kuma Itama Dan jaraba har yanzu taki hakura dashi, neehal tace ke waye zai samu opportunity din data samu kuma yayi wasa, ai samun miji kmr kabeer sai me tsananin SAA da kuma rabo, Sbd kabir allura cikin ruwan kogine, kinga kuwa sai me tsananin rabo ne zai sameshi kema kinyi shirme da kikayi fushi kika fito daga dakin, Aida saiki tsaya Ku buga da ita, my sis inaso ki sani kabeer yanada wata baiwa da ba kowanne namiji bane yake da ita, Sbd haka ki tashi ki koma dakin ki bashi duk wani caring daya kamata, kinji ko nace to dariya tayi tace Mrs kabeer saina kara jinki nace ok thank you my sis kicewa ammi I miss her so much. Ina kashe wayar na mike na kara gyara fuskata, sanan na fice zuwa dakin, INA shiga ya Bini da wani irin kallo ko zama banyi ba nace me kake sha'awa ci a dinner? Yace yimin cuscus da vegetable soup to kawai nace na fita daga dakin, cikin 30mint nagama komai, har zobo me hade da kankana nayi masa, INA kaimishi na koma daki nayi sallar magrib shima ya fita yayi salla zuby kuwa Dan gadara a dakin tayi salla. Ban koma dakin ba saida nayi sallar isha'i INA shiga naga zuby tana serving dinshi abincin wani irin bakin ciki naji ya cika min zuciya juyowa tayi tai wata dariya sanan tace sannu da kokari, cewa nayi bari nayi assisting dinki tunda ke kinyi girki kin gaji, murmushin yake nayi nace karki damu duk daya ne ai, zama tayi a kusa dashi tana bashi lbri shi kuma yana cin abincin yana dariya, yama manta da INA wajen danaga haka kawai saina hau online na fara charting da yan grp dinmu na maman aysha grp muka fara hira sainaji zuciyata tayimin dadi. Time to time yake dagowa ya kalleni, ni kuwa na manta dasu. Bayan ya gama yace Aysha abincin yayi dadi thanks allah yasaka da alkairi, ba tare da na dago ba nace amin. Shiru dakin yayi na yan mintuna sanan zuby ta mike tace honey zan tafi saina dawo gobe, yace to Allah ya kaimu.

Tana fita ya dawo kusa dani ya zauna Aysha naga kmr kina fushi dani, ko nayi miki lefi ne? Nace Aa, are you sure? Nace eh, OK to akwai mgnr da nake so muyi dake nace to, mun yanke decision da zuby zaa daura auranmu da ita nanda 3wks, daga baya sai ayi fixing date din Biki, kuma  ranar bikin zaa daura auran mu dake kinga sai a hada bikin lkc guda ayi, so ya kika gani? Tunda ya fara maganar zuciyata take harbawa da sauri, na nemi yawun bakina na rasa har saida yakai karshe, kasa cewa komai nayi har saida ya rike hannuna cikin unique voice dinsa da yake kashe ni da ita yace Aysha kinyi shiru? Da kyar na iya cewa me kake so nace? Cemin fa kayi kun yanke decision, so ai no need kaji view dina, tunda kana ganin hakan yayima kawai shikenan, mikewa nayi nace nima zanje na tafi saida safe harna fara tfy ya fisgoni na fado jknsa harna kusa fama masa hannunsa, har yanzu baki bani amsar abinda nakeso ba, Aysha kinsan zuby ita na fara so kafin ke kuma nayi mata alkawarin aure tunda dadewa so kinga bazai yiyyu yanzu nace bazan aureta ba so don Allah kiyi hakuri na aureku Ku biyun, cikin tsananin bacin rai da tashin hankl nace don Allah kabeer ka kyaleni da mgnr nan, ka bari idan nazo gobe ma karasa ni yanzu bacci nakeji, INA kokarin zamewa daga jknsa ya manna min kiss sanan yace I Luv you Aysha, da kyar ya sakeni na tafi daya daga cikin body guards dinsa ne ya kaimin su basma mota, saida na saita kaina nayiwa su mum da aunty Salma sallama, INA shiga mota kuka me karfi ya kwacemin, INA driving INA kuka da kyar na samu na karasa gd

Maman Aysha
[10/14, 20:32] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓

2⃣2⃣5⃣➖2⃣3⃣0⃣

Ina shiga na sami mum da dad a zaune suna kallo saida na kwantar dasu junior a daki sanan na dawo gunsu muka Dan taba hira, na fada musu gobe zan tafi Kaduna dad yace Allah ya kaimu, amma naga kmr ranki a bace yake, ko munyi miki lefi ne? Dariya na kakaro nace aa dad bacci nake ji ne, Mum tace to ai gwara kije ki kwanta, ya me jikin nace da sauki Allah ya sauwake nace amin saida safe suka amsa gabdayansu

A kwance nake amma bacci ya kauracewa idona, rabonda na shiga tashin hankali irin na yau tun ranar dasu dad sukace basu suka haifeni ba, meyasa kabir zaimin haka? Ashe dama shi mayaudari ne? Wata zuciyar ce tace min dama ba sonki yake ba tausayinki yake Sbd rasa parents dinki da kikayi, yes hakane, tabbas zuciyata tayi gaskiya dama kabeer tausayi na kawai yake kuma yanzu tunda na gansu,  ba maganar so kenan, ya salam yanzu ya zanyi kenan? Bazan taba iya son wani mutun ba inba kabeer ba, shikenan saidai na mutu banyi aure ba kenan? Kukane na fara cike da tausayin kaina, Daidai nan abba ya kirani a awaya yace Aysha yaushe zaki dawo ne? Zaman yayi yawa haka a hankali nace gobe zan dawo insha Allah, to ame zaki taho? Ko a commercial car ma Abba, aa zan tru driver da neehal su daukeki  nace to nagode Abba, amma naji muryar ki kamar kinyi kuka? Na fara bacci ne, OK to saida safe, nace Allah ya kaimu. Da kyar na samu wahalallen bacci ya daukeni

Ita kuwa zuby tana fita daga gidansu kabeer ta kira malaminta a waya, hlo mallam aikinka yana kyau domin kuwa na fara samo kanshi saidai na fuskanci indai bata kusa dashi to hankalinsa da tunanin sa gunta yake tfy, dariya yayi yace karki damu akwai wani zazzafan hadi da zanyi miki amma sharadinsa dole lkcn da zakiyi amfani da maganin ya zamana suna tare, kuma kwana uku zakiyi kina amfani dashi, ita dariyar tayi tace ba matsala mallam ai tare muke zaman jinyar da ita, so kullum saitaje gdn anan sukayi sallama ta kashe wayar.

Washe gari
 Da wuri na tashi nayi duk aikin daya kamata, sanan nayi wanka na fito falo muka zauna munata hira da mum da lkcn yin abincin rana yayi na shiga kitchen na dafa sanan na dawo hira muke sosai da har naji damuwa ta ragu sai wajen 12pm su neehal suka karaso da gudu nayi hugging dinta ta durkusa tagaida mum, sanan muka barke da hira tare mukaci abinci aka kaiwa driver ba ma nasa, sai wajen 1:30 mukayi sallama da mum muka tafi Sbd daga gdn su kabeer zamu wuce, tace min suma next WK zasu je Kaduna da dad, sabd sunaso su gaisa da family mu

Muna zuwa gdn muka sami falonshi a cike, zuby na zaune a kusa dashi ko kunyar su mum bata ji ita kuwa aunty Salma tun wajen 7am tayimin waya tace ta wuce abj, a tare muka durkusa nida neehal muka gaishe da mum, nace ya me jiki tace mejiki ya warke kinga yanzuma bamu Dade da dawowa daga asibiti ba, ancire POP dinma, kuma anyi x_ray ba matsala nace to Allah ya kara sauki tace amin, kallon neehal tayi tace yaushe kika zo? Tace dazu yasu ammi? Tace suna nan kalau, sai alkcn nakai idona kansa na gaisheshi na masa ya jiki, neehal ma ta gaisheshi tana tsokanar sa mum ce tace min Aysha mutumin naki fa yaki cin abinci wai sai naki yakeso, a zuciyata nace Dan renin hankali baya sona amma yana son abinci na,Aida zubyn saitayi mishi, idan na tafi naga yanda zaiyi.....amma a fili sai nace to mum a kunyace nace me zaa dafa mishi? Tace tambayeshi, juyawa nayi muka hada ido, ya salam gasky kabeer akwai zallar kyau, anya zan iya rayuwa bashi kuwa? Shiya katse min tunani da cewa dambun shinkafa nake so, nace to, tare muka tafi kitchen da neehal ta tayani mukayi girkin tare muna kamallawa na kawo mishi saida yaci ya koshi da lkcn sallar laasar yayi mukaje mukayi, muka kara dawowa falon sanan na kalli mum nace mum zamuje mu tafi kar dare yayi mana fuskarta cike da mamaki tace dama yau zaki tafi nace eh, amma baki fadamin ba? Nace wallahi sai jiya da daddare na tsara tafiyar to shikenan ai kinyi kokari Allah yayi miki albarka nace amin tace bari na dauko sako ki kaiwa amminku nace to,  a rude zuby tace haba ke kuwa Aysha ki daure ki kara ko 3days mana kinsan abincin ki kadai yake iya ci, don Allah ki taimaka ki zauna murmushi nayi nace ba matsala aunty zuby ai kina nan, so you should take over neehal ce ta fara fita nima nabi bayana har naje bakin kofa yace Aysha da wata irin murya, juyowa nayi ba tare da nayi magna ba, kawai sainaji yace kowa na falon nan ya fita inaso zamuyi sallama, nan take kowa ya fice harda zuby karasawa bakin kofar yayi yasa key ya rufe, sanan ya juyo ya rike hannuna yace meyasa zakimin haka aysha? Idan kika dauke mum ba wacce nake so a duniya kamar ke, kodan Sbd mgnar Dana fada miki jiya zaki tafi? Nace aa, to meyasa zaki tafi? Aidama nace idan ka sami sauki zan tafi, kuma you're stable now, amma kinsan bazan iya jure rashin ki ba ko? Cikin kuka nace budemin na tafi nima iyayena suna bukata ta a kusa dasu, na gaji dajin mayaudaran kalamanka kabeer, karya ne baka sona yaudarata kawai kake, da kana sona bazakace zaka hadani da wata ba inaso kasani har abada bazan iya auran ka kana tare da zuby ba Sbd haka ni na hakura dakai, ka manta dani a rayuwar ka INA maka fatan alkairi dakai da zuby bude min kofa na tafi, mutuwar tsaye yayi yana kallona cikin daga murya nace ka budemin nace,, jiki ba kwari ya bude min na fita da gudu

Maman Aysha.




[10/15, 21:40] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓

2⃣3⃣0⃣➖2⃣3⃣5⃣

Ina fita da sauri na shige mota INA kuka ko sakon da mum tace zata bani sai neehal ta bawa su duk a zaton su Sbd zanyi missing din adon gari ne yasa nake kuka, mum har cikin motar ta shigo tana rarrashina daga karshe mukayi sallama muka tafi. Tunda muka dau hanya nake kuka, neehal tace haba Mr Luv wai rabuwa da Kabeer din ne yasa kk ta wanan kukan? Ba haka bane sis kabeer yace min wai mu biyu zai aura nida zuby, INA tsananin son kabeer bazan iya sharing dinshi da kowa ba, wallahi sis Dana aureshi yanada wata matar gara na hakura dashi koda sonshi zai zama ajalina.....ke meyasa bakida hankali ne? Neehal ta katse ni ya kike nema kiyawa kanki shirme? Kin sami mijin da kowacce mace zatayi mafarkin samu amma zakiyi watsi da damarki, to wallahi gwara ki canja shawara, baya sonki ya mutun taki alokacin da baki da gata, Sbd tsananin sonki dayake ne lkcn da mum dinsa tace zata hadani dashi yakira hydar ya fada masa, kuma baki kula da tashin hankalin daya shiga ba dazu da kikace zaki tafi? Wanan  girkina yake so bawai Sbd rabuwa dani bane, dalla yimin shiru girkin naki ma ai don yana sonki yasa ya damu dashi, shiyasa akace idan kafi mutun ko yayane saika fishi hankali zunburo baki nayi nace kaji sis da 20 mint fa kawai kika fini, idan ma da second ne na rigaki shan iskar duniya, kuma na fiki hankali. Sai wajen 5pm muka isa gd

A bangaran kabeer kuwa tunda na fice ya rasa abinda yake masa dadi, zama yayi akan kujera wasu zafafan hawaye suna zuba a idonsa harsu mum suka koma  dakin baya cikin hayyacinsa, a kusa dashi mum ta zauna tanata aikin rarrashi take, dakyar ta samu yayi shiru ganin mutane sun fara cika dakin kawai saiya mike yace  duk Wanda yazo dubani nagode, Sulaiman ni zanje na kwanta duk na sallame Ku saida safe, da hanzari ya fice daga dakin ya koma dakin mum ya kwanta, wayar shi ya dauka ya fara kiran Aysha yaji ko sun isa gd lpy amma batayi picking ba, saida yayi wajen 10 missed call bata dauka ba hankalinsa ba karamin tashi yayi ba, cikin rudani ya fara kiran no neehal tana dauka yace my sis kin wuni lpy? Tace lpy kalau ya kuka isa gd lpy kanina, na kira Aysha bata dauka ba don Allah ko zaki hadamu tace to gata, tashi nayi na koma dakina, Aysha kinaso sonki ya kashe ni ko? Meyasa kk treating dina haka, kinsan ba zan iya rayuwa ba tare dake ba meyasa kike wahalar dani? Ashe bazaki iya yimin alfarma ba kenan? Aysha ko kin daina sona ne? Tsananin son da nake maka ne yasa na shiga halin da nake ciki yanzu, INA sonka kabeer bazan iya jure ganinka tare da wata matar ba, INA tsananin kishinka kabeer, wallahi Dana aureka INA ganin ka da wata matar gara na hakura ciwon sonka  ya kashe ni.....don Allah ki daina fadin wanan mgnr Aysha, indai Sbd Zuby ne na fasa auranta, yanzu hanklinki ya kwanta? Ba kunya nace eh, yace are you sure? Nace yes dariya yayi yace Aysha kenan dama haka kk da kishi gabadaya kin daga min hnkli, Nima dariyar nayi nace ba abinda ba zanyi ba akanka yace ko? Kuma gashi inada yan mata buhu buhu, dariya na karayi nace na daura belt din yaki dasu ai, rufe min baki da allah bayan guda daya ma ta gagareki, wallahi Aysha da nakasa bacci, amma kinga yanzu iam OK so bari na barki ki kwanta Sbd kinyi tfy kin gaji I Luv you, nace I Luv you too. Yana kashewa na shiga na bawa neehal phone dinta tace munafuka sai yanzu kuka gama wayar, dariya kawai nayi na tafi na kwanta

Maman Aysha
[10/16, 09:24] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓

2⃣3⃣5⃣➖2⃣4⃣0⃣

Yana gama waya dani ya kira zuby kmr abin arziki bayan sun gaisa ya fara yimata nasiha, daga karshe yace tayi hakuri ya fasa auranta a zabure ta mike tsaye jitayi kamar ya watsa mata ruwan zafi wallahi baka isa ba kabeer, kai ka isa ka yaudare ni saida kaga lkcn auran ya kusa sanan zakace ka fasa,  ban yaudareki ba zubaida Sbd dama nida ke muka yake rana suranmu ba tare da iyayenmu ba, kin taba ganin inda akayi aure iyaye basu shiga ciki ba? Inayi miki fatan alkairi Allah ya hadaki da Wanda ya fini kawai ya kashe wayar. Cikin tsananin rashin hnkl tayi wurgi da wayar nan take ta wargaje a kasa, kuka take sosai wallahi ko abinda na mallaka zai kare saina aureka adon gari Allah ya kaimu gobe na koma wajen mallam, kasa baccin kirki tayi Sbd tashin hankalin zatayi loosing din adon gari

Washe gari
Zubaida ce zaune a haban bokanta alagafarta boka ko nawa ne zan baka, nidai kawai duk yanda zaayi na mallaki kabeer, ba zai yiyyu ba hhhh aijani👹 Dan lakiskis yace kin bata aikin ki, Sbd kin kauce shardin daya baki akan amfani da maganin daya kawo miki, yanzu boka ba abinda zaka iyayi kenan? Gaskiya ba abinda zan iya, kuma ko wani wajen kk je bazakiyi nasara ba Sbd yaron yadawo da halinsa nayin adduar tsari, INA ganin shiyasa tun farko bamuyi nasara sosai ba, jiki ba kwari ta koma gd

2 days later
Muna zaune da ammi a falo na Dora kaina akan cinyarta kamar daga sama mukaji muryar mum din kabeer tana sallama, da rawar jiki ammi ta tare ta ta zauna, a kujera akunyace na gaisheta sanan na shiga kitchen na fara hado mata abin motsa baki, dakin ammi nakai mata suka koma can suna hirarasu ta aminai har Abba ya dawo mum tayi mishi bayani tazo ta fada musu ne yan uwan dad dinsu kabeer zasu zo Neman aurena , Abba yace ba matsala, saida ba wajena zasu zo ba wajen babanta na kano zasu, Sbd haka su fadi ranar da zasu zo sainayi mishi bayani tace to shikenan Allah ya tabbatar da alkairi yace amin.

Haka kuwa akayi sunje sun sami dad, kuma an yanke ranar auren lkc guda Dana neehal. Tunda ga lokcn aka fara shirye shiryen biki Abba ya saki kudi yace duk wani Abu da akewa yan gata muma yanaso ayi mana, an dauko masu gyaran jiki tun yanzu sun fara gyramu
Tun kafin bikin munyi kyau kamar asace mu
Su aunty Salma sunkai kayan lefena gdnmu na kano fadin kyau da tsaruwarsa  baa magna me krtu kayi imagining kawai, ranar da aka kai kayan zee har Dan karamin hauka tayi, ta ringa fadin maganganu wai shikenan ta rasa kabeer, ita bazata yi aure ba indai ba kabeer ta aura ba dakyar mama tayi controlling dinta ta hakura

1 WK later
Muna zaune da kabeer a falon gdnmu na kd ya kalleni yace beauty kinga yanda kk koma kuwa? Da na rasa ki da nayi babbar asara ke kullum kyaunki karuwa yake ne? Dariya nayi nace duk kyau na ai ban kama kafar adon garin yan mata da samari ba, cikin shagwaba nace ni idan anyi auran ma bansan ya zanyi da yan matanka ba, Sbd nasan bazasu daina binka ba, ni kuma inada kishi kallon kwayar idonsa nayi a hankali nace bansan wane irin so nake maka kabeer, wallahi komai zai iya faruwa dani indai akan sonka ne. Janyoni jikinsa yayi, yayi hugging dina sosai yace karki damu aysha insha Allah adon gari naki ne ke kadai, Nima bazan taba iya hada sonki da wata ba Aysha, kuma kanki kika sani amma nafiki sonki ranar da kika taho kk barni saura kadan na margaya fa, dariya nayi nace aikuwa Dana bi bayanka shima dariyar yayi yace I Luv you wit all my heart Aysha, zamuje mu wuce sai ranar biki kuma, har bakin mota na rakashi dakyar mukayi sallama ya tafi

Maman Aysha


[10/18, 13:39] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓

2⃣4⃣0⃣➖2⃣4⃣5⃣

5/10/2016
A yau laraba ne aka fara gudanar da shagalin bukinmu, mum dina ta kano tun Monday ta taho aka fara shirye shirye, mum din su kabeer ma da aunty Salma gobe zasu taho da ango elbash ma ya kawo aunty rahama sai angama biki zata tafi. Da kauyawa day aka fara, adon gari yayi inviting arewa 24 sukazo suka dauka idan kaganmu saika rantse daga kauye muke, amma angwaye basu je ba, Dan asharalle aka dauko mana mana muka sha rawa sai dab da sallar magrib muka dawo washe gari alhamis akayi Arabian night seventeen hotel akayi wasu shegun Arabian gown mukasa wadda kudinta zaikai 100k tawa pink ta neehal red su kuma su adon gari da hydar fararen jallabiya suka saka da hula wanda kudin su zai kai 150k munyi kyau har mun gaji saika rantse da Allah daga kasar larabawa muke more especially nida adon gari dake mu farare ne kuma ya manna Dan siririn tabaraunsa a ido Wanda yake kara masa kyau, taro akayi na gani na fada maheer ne yazo yayi waka awajen, Aljazera TV ne suka dauki program din ansha budiri anyi rawar larabawa kamar me, can na hango yan Maman Aysha GRP sunata casa rawa Abu nasu maganin a fadesu su zaj har mayafin abayarta yana faduwa Sbd rawa sai wajen 11pm aka tashi, a gajiye muka koma gida, kabeer da friends dinsa kuma a cikin hotel din suka kwana washe gari Friday kuma akayi kamu da yamma a compound din gdnmu dake yanada girma kuma anyi mishi decoration  Dan ubansu da daddare kuma aka tafi Indian night dressing din India mukayi da saika rantse daga can mukazo, ammi duk Wanda ya kallemu  saiyace masha Allah. Yauma a seventeen din akayi wakilan mbc Bollywood ne suka dauki program din suka haska wato me karatu saika rantse a kasar India akayi bikin, fadin kyau da tsaruwar abin kuwa bata lkc ne, wato abin baa cewa komai fili na musamman aka budewa Aysha da yan Maman Aysha grp akasa musu waka suka ringa tikar rawa kabeer ya ringayi musu liki da dollars. Yauma sai wajen 10:30pm aka tashi.

8/18/16
A yaune da misalin 11am daruruwan mutane suka shaida daurin auran Kadija Abdullahi Idris makarfi da angonta Aliyu hydar, sai kabeer Muhammad BAGAUDA da amaryarsa Aysha Ahamad TURAKI daurin auren da yatara many mutane harda president of Nigeria, duk wani gdn television da masu buga jaridun daka duba shagalin bikin ake nunawa wasu daga cikin yan matan adon gari da besan da zamansu bama har suma suka ringa yi sbd tashin hankali, wasu kuma sun dauki alwashin sai inda karfinsu ya kare na ganin sun mallake shi, yayinda wadansu suke ganin nafi kowa SAA a duniya Dana mallaki allura cikin ruwa, kuma adon garin yanmata da samari. Karfe 12 rana Abba yasa aka kiramu yayi mana nasiha me shiga jiki, sanan  gabadayanmu muka dau hanyar kano Sbd mum dina(Haj Jidda) ta shirya walima a Amneef, ta gayyaci yan Uwa da abokan arziki mallam Aminu daurwa ne yazo yayi waazi a wajen, shima sai daf da magrib aka dawo, sanan washe gari Sunday mum din su kabeer ta shirya mother's eve a meenat kowa da gate pass ya shiga hall din, anyi buduri anyi shagali an warwasa kamar me, ana 6:30 taro ya watse ana tashi su neehal da ammi da sauran yan Uwa suka dauki hanyar Kaduna Sbd a Daren za a raka kowa dakin mijinsa dakyar aka banbare ni daga jigin ammi da neehal, haka muka rabu suna kuka ina kuka, wajen 9pm jerin gwanon motoci sukazo kofar gdnmu na kano daukar amarya dama nayi wanka na shirya cikin wani lallausan boyel sky blue da touch na red ajiki, na yafa mayafi red mum ta dauko min wasu hade_haden kayan mata tabani nasha, sanan ta kamani ita da aunty Salma muka fita, gdn mum din kabeer aka fara kaini sanan aka wuce dani dankareren gdna dake nasarawa GRA

Maman Aysha
[10/18, 20:58] Amina Yakubu: 🏓🏓🏓KABEER🏓🏓

2⃣5⃣0⃣

Bayan yan kai amarya sun tafi aka barni ni kadai shiru kabeer be dawo ba, phone dina na dauka na fara kiran neehal bayan mun gaisa tace mun sauka lpy Aysha, kinga ma yanzu Wanda suka rakoni suka tafi iyayenmu sunyi mana kokari saidai muyi musu addua Allah ya saka musu da alkairi, misali ma ke aysha me iyaye hudu, kinsan fa dad da mom dinki part guda suka dauka acikin gdnki suka zuba komai da ake bukata, gaskiya an kashe dukiya a gdnki dake yafi nawa girma sosai dariya nayi nace Allah ya barmin ke my sis, wato ni iyaye hudu ne dani ko? Ita dariyar tayi tace eh mana, uhm ni karki dameni da surutu naji motsin hydar ya shigo, ke duk zumudin da kabeer yake har yanzo be shigo ba? A sanyaye nace eh wallahi, a wancan lkcn yayi winning ta wajen banbance tsakaninmu dake, a yanzu kuma hydar yayi winning ta wajen zuwa gun amaryarsa da wuri, wata shegiyar dariya tayi tace bye sai mun Kara waya.

Bakin ciki ne ya kamani to me kabeer ya tsaya yi har yanzu be shigo ba tun INA ganin abin kamar wasa har tafiya tayi nisa, raina idan yayi dubu ya baci gashi tsoro ya fara kamani ni kadai agidn, wasu hawaye naji sun fara bin kumatuna na, nayi dialing no shi naji switch off kawai saina tashi na cire kayana NASA wata armless gown purple nayi wanka da turare na kunna A/C dakin nayi addua na kwanta

A bangaran kabeer kuwa akwai friends dinsa da suka zo daga England, bayan an tashi daga mothers
eve ya kaisu hotel din daya kama musu, ya dawo gdnsu ya shiga part dinsa yayi wanka ya shirya cikin wani farin lallausan tissue yadi Dan wajen 40k yayi wanka da turare, sanan ya shiga yayiwa mum sallama ya kama hanyar gdnsa zuciyarsa dauke da zumudin ganin aysha, Sbd yacewa friends dinsa kowa ya tafi makwanci sa baya bukatar rakiya. Yana daf da kofar gdnsa Michael daya daga cikin bakin da sukazo daga England ya kirashi a rikice yake fada masa asthma John ta tashi, kuma ya manta inhaler sa a gd, kuma is lyk kamar baya breathing ma, cikin tsananin tashin hankali ya juya kan motar ya koma hotel din daya saukesu ya dauko marar lpy suka nufi asibitin Dr marwan friend dinsa nan take aka fara bashi emergency care, hankalin adon gari idan yayi dubu to ya tashi, Sbd ga tunanin aysha ya barta ita kadai a gd, ga kuma John mutumin da ya taho musamman tun daga England yazo bikin shi yana kwance rai a hannun Allah, kuma gashi wayoyinsa a kashe suke. Basu suka samu numfashinsa ya dawo normal ba sai wajen 11pm, yana mayar dasu masaukinsu ya taho gida a sukane

Harna fara bacci tsoro yasa na farka, zama nayi na rakube a gefen gado banda risgar kuka ba abinda nake, kamar anjefoshi ya shigo dakin cikin dimuwa ya karaso wajena zai rikeni na matsa karka sake ka tabani kabeer, wanan shine sakamakon soyayyar da kake ikirarin kana yimin? Wanan shine son ka wulakantani a Daren da kowacce mace take mafarki a rayuwarta, tun wajen 9:30 hydar din neehal ya koma gida, amma kai sai yanzu kake shigo min? Kabeer ko kanada wani boyayyen hali ne da bansan ka dashi ba? Fisgoni yayi na fado jikinsa yayi min wani irin wawan hugging don Allah kiyi hakuri beauty nasan dama ba irin zargin da ba zakiyi a ranki ba, wallahi matsala aka samu ba a son raina haka ta faru ba, don Allah ki cire zargina aranki kinsan INA sonki, kuma yau special ranace Dana Dade INA mafarki kuma yanzu Allah ya nuna min ai kinsan bazanyi da wasa ba ko? Murmushin da yake kara masa kyau yayi sanan ya zaunar dani akan gado ya fara bani lbrn abinda ya faru, daya gama yace INA fata kin  fahimci mijin ki Aysha? Shiru nayi banyi magna ba kneeling yayi yace Aysha don Allah ba don ni ba kiyi hakuri kinji? Ko kallon shi banyi ba kawai saina ga ya daukeni ya fice dani daga dakin ya nufi bed room dinsa dani, akan lallausan gadon sa ya ajiye ni sanan ya fada toilet ya kara yin wanka yana fitowa ya dauko 3 quarter wando da armless Riga yasa, ya feshe jikinsa da disigner turaren shi sanan ya janyo wasu ledoji yace sakko kici abinci, still ban tanka mishi ba hawowa gadon yayi yace haba Aysha har yanzu baki hakura ba ne? Sai kuma naji tausayin sa nace na hakura, to sakko muci abinci cikin shagwaba nace ni nakoshi saida naci abinci kafin na shigo gdn nan, are you sure? Nace uhm, janyoni jikinsa yayi yace nima na koshi mu kwanta, cikin shagwaba nace to ni ka matsa daga kusa dani bacci zanyi yana darya yace Aysha nifa mijinki ne yanzu, amma kk korata zan kara magna ya hade bakina da nashi yana tsotsa at d same time kuma ya fara aikamin da wasu sakkoni da bazan iya fadawa me krtu irin su ba, mu kwana lpy Aysha da kabeer

Maman Aysha



🏓🏓🏓KABEER🏓🏓

2⃣5⃣5⃣➖2⃣6⃣0⃣
Final episode

Ba karamin galabaitar dani kabeer yayi ba, ba irin kukan da banyi ba gashi be barni nayi bacci da wuri ba sai wajen 1:30am na samu nayi bacci dakyar.

Inajinsa ya tashi yayi wanka ya fita sallar asuba amma na kasa tashi, har ya fita ya dawo INA kwance, gadon ya hau yana min mgna a hnkli Aysha har yanzu baki tashi ba? Yana kokarin dauka ta na bude ido karka tabani zan iya tashi da kaina, fuskarsa dauke da murmushi yace to tashi, da kyar na yunkura na mike wani mahaukacin jiri yana kwasata, gashi na hana kabeer ya rikeni, haka na lallaba na shiga ban dakin INA shiga naga ya hadamin ruwan ya fice saida na gasa jikina sosai, sanan nayi wanka na fito, direct dakina na wuce nasa kaya, wata English gown nasa purple color me karamin hannu sanan nayi salla bayan nayi addua naje gbn mirror nayi simple make up, INA cikin fesa turare naji jiri yana kwasata, na tafi looo zan fadi....shigowarsa dakin kenan ya tafi da gudu ya tareni na fada jikinsa, cak ya daukeni ya maidani dakinsa ya kwantar dani akan gado, cikin tashin hankali yace Aysha me yake damunki? Nace kaina ne yake ciwo, Sannu kinji duk laifina ne,ni nayi causing din komai bari na kira marwan yazo ya dubaki nace to, yana mishi waya saiga shi yazo allurai yayi min ya rubuta mgni nan take bacci me nauyi ya daukeni ko break fast na kasa, zama yayi ya zuba min ido yana kallona kamar yau ya tafa ganina phone dina ce ta fara ruri yana dubawa yaga neehal ce dauka yayi yace sis dinmu gud morning, morning kanina, INA Aysha? Wallahi...sai kuma yayi shiru, meya faru kanina? Ko bata da lpy ne? Eh yanzuma bacci take, eyya to shikenan idan ta tashi zan kara kira, Allah ya sauwake yace amin.

Sai wajen 1pm na farka naje nayi brush, sanan ya kawo min abinci naci haka muka wuni a ranar banda lallabani ba abinda yake, baki kuwa sai zuwa suke saidai shi ya fita yace musu INA bacci

1 WK later
Yau na fara girki, tun 4pm na shiga kitchen nayiwa kabeer tuwon shinkafa da miyar egusi sanan na hada mishi zobo me kankana da cocomber a ciki nasa a fridge, zuwa 5pm nagama komai dama yaran da suke min aiki sunyi sharar yamma duk da gdn ba datti  yake ba, sanan na kunna lafiyayyun turaren wuta a gdn, daaki na koma nayi wanka na shirya cikin wata English gown nasa me two pieces ta saman doguwa ce har kasa yellow me karamin hannu, yar cikin kuma body hug ce long sleeve ita kuma red color twisting ne akaina sun zubo har gadon bayana nayi kwalliya a fuskata, Dana kalli kaina a madubi ni kaina nasan nayi kyau Sbd samun me kyau na ko akasar India sai an sai anyi screening kafin a samu 😀lol. INA cikin fesa turare naji ana sallama ina fitowa naga su Yaya zee ne da friends dinsu su wajen bakwai, da fara'a ta na tare su dake falo uku ne a gdn saina kaisu pink falo Suka zauna, muka shiga jera musu kayan motsa baki nida yaran da suke min aiki har saida Yaya zee tace ya isa haka sanan na zauna muna hira suna cin abincin, Daya daga cikin su ce tace sanyin A/C yayi mata yawa saina mike zan rage musu karfin, sanye yake da yellow shirt da red jeans, shirt din anyi mata rubutu da red pen hankalinsa gabadaya akaina yake ya shigo falon yana wakar winner wowo winner, winner wowo winner yana wata shu'umar dariyarsa da take jefa duk me kallonsa a wani yanayi, hugging dina yayi sosai sanan yace my angle guess what? Iam....be karasa ba nace masa su Yaya zee ne suka zo, sai a lkcn ya kula dasu, kuma nan take smiling din da yake fuskarsa ya dauke Sbd ya saida su gadayansu ba wacece batace tana sonsa ba, cikin shan mur yace sannunku da zuwa, suka amsa tare da gaishe shi ko amsawa beyi ba ya kalleni yace bari naje na jiraki aciki nace to, yana fita Yaya zee tace muma tafiya zamuyi Aysha, nace da wuri haka? Eh, karki damu zan dawo saida na rakasu har waje sanan mukayi sallama suka tafi.

Daya daga cikin su me suna rasheeda tace meyasa masu kudi ko kyau basa adalci ne? Kamata yayi ace idan mutun yanada kyau, saiya samu wacce ba kyakkyawa sosai ba ya aura, shi kuma me kudi ya ringa auran yar talaka, amma now a days auran karawa me karfi karfi ake, ku duba kuga Aysha da Kabeer kowa ya naji da kyau, kuma gashi Allah ya taimaketa kallo daya zakaiwa adon gari ka gane yana tsananin sonta, muma Allah ya hadamu da mazaje na gari Wanda zasu so mu, sauran suka amsa da amin

Ni kuwa suna fita naje na samu kabeer a daki nace wai me ya faru ne naga soul mate dina yana farin ciki? Janyoni jikinsa yayi yace kamfanin Dana bude na atamfa Hilton ya kammala yanzu bikin bude shi kawai zaayi murmushin da nasan yanaso nayi nace congratulation The only handsome in d world, Allah ya nuna mana ranar cikin farin ciki yace amin.

     3 years later
Zaune nake a wajen da aka tanada na shakatawa acikin gdn, gefena kuma kyakyawar yarinya ce me kama da kabeer yar kemanin 2yrs akan keke tanata dariya tana daga min hannu, banyi auni ba kawai naga ta fadi kasa kafin na karasa na dauke ta harya Riga ni ya rungume ta yana rarrashinta da mamaki nace yaushe ka dawo? Wani lallausan smiling yayi yace yanzu, hugging dina yayi cikin cool voice dinsa yace gaskiya yau ya kamata a samawa Nana kani ko kanwa, dariya nayi nace iam already conceived saidai ka tayani addua Allah ya saukeni lpy, are you sure? Nace yess, alhamdulilla, kiss ya mana min sanan yace fadamin kasar da kk so muje? Nace Muje Istanbul, daga nan mu wuce Saudi Arabia yace duk yanda kk ce haka zaayi aysha, I Luv you wit all my heart, nace I Luv you too, muka shiga cikin gd cikin nishadi.

Alhamdulilla anan na kawo karshen Kabeer Ina mika godya ga masoyana more especially members din Maman Aysha group I Luv you all

Maman Aysha

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *