Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, June 4, 2018

MARAICHI Complete latest hausa novel

adsense here
[14/1 12:54] Zeeenaseeer: 🌳🌳.      ⚜.       🌳🌳
  🌳.                         🌳
              👑👑
             
              🌳🌳
                🌳
      MARAICHI❣
             NA
 Zainab Naseer Sarki
     (Zeenaseer😘)

🎊🎊🎊🎊🎊🎊🎊
    I dedicated dis page to oll by fans Lov u so much Fata nagari gareku kuma ina muka murna da shigowa sabowar shekara Allah kasa munshiga cikinta tareda tarin alkhari daga Allah ubangiji subhanahu wata'ala.
        Wish u appy new year and wlcm to 2017.
    🎉🎉🎉🎉🎉🎉🎉
Another new year is here!
Another year to live!
To banish worry,doubt and fear,to love and laugh give🤗
     HAPPY NEW YEAR
     💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼😂😘.

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM.

0⃣1⃣

Hadarine ya hado garin gaba daya yayi duhu,ga iska me karfi anata faman yi mutane sai faman sauri suke kar ruwa ya iske su.
Wasu suna gudu wasuna hada kaya.
   Sai faman buga kofofin gidaje iskar akeyi.
Wani gida na hango gidan babbane ba laifi kofar gidan safe yake da siminti sai kofa maidan fadi,irin gidan nan ne dasai kin huce soro tukun zaki shiga cikin gidan.
     Tsakar gidan babbace sai dakuna guda hudu acikinsa sai kitchen da ban daki.
    Saikuma wani daki hanyar fita daga gidan wato daga cikin soran.
    An malale tsakar gidan da siminti shima sai rijiya daga can nesa.
   Ko wani daki ciki da rumfane.
Saka makwan iskan da akeyi ne gidan babu kowa cikinsa da alama duk suna cikin daki.
    Dakin farko na leka zauna cikin falon na hango wata yr yarinya saman kujera ta takure da alama sanyi take ji kyakyawace tana da gashi amma fatar jikinta ba fara bace saide akirata da chocolate sanye take da riga fara me hannun singlet da chain a huyanta.
      Saikuma wata yr karama akwance akan dayar kujerar da alama bacci takeyi shekarunta fazasu haura uku ba.ita kuma ta farkon nata shekarun basu gaza goma zuwa sha daya ba.
     Cikin dakin na shiga wata mata na gani wanda shekarunta fasu gaza 30 ba kyakyawa fara tas dauke take da tsohon ciki haihuwa ko yau ko gobe.
   Tsaye take jikin wardrobe da alama kaya zata dauka.
Fitowa tayi falon ta zauna kan daya daga cikin kujerun.
    Nan ruwa ya sauka ba tsayawa sosai akeyin ruwan tareda walkiya.
     Sapna matar ta furta tana kallon yar tat dake zaune saman kujera.
   Taso ki amshi wannan rigar ki sanya tunda naga kamar garin ya fara daukar sanyi.
Kuma ki dauki hularki ki sanya bakya San zama da dankwali ko kadan.
    Mikewa tayi tareda kara sowa wajan matar.amsar rigar tayi tareda da juyawa zata koma ta zauna.
     Riko hannun ta matar tayi tare da fadin me nene kuma sapna.
    Hawaye ne suka fara bin kuncinta kanta akasa tama kasa kallan matar.
    Hannun ta tasanya ta goge hawayen tareda fadin mama cikin muryar ta me sanyi Safiya ce ta kwashe mun littattafaina gaba daya wai ba zanyi karatu ba ta zubar min dasu akan hanya da zamu dawo daga makaranta dan kar nayi pass a exam na huceta.
      Amma meyasa baki gayamin ba tun daxu.
   Cewa tayi inna fada gobe sai ta taru da frnds dinta sun yimin doka.
    Haba Sapna duk da nasan safiya yayar kice be kamata ki tsaya kina yimata kukaba.
Gaba daya wannan miskilancin naki haushi yake bani wlh.
Kuma kinsan halin su sarai to Wallahi ki kiyaye ni narasa wata irin jarabace wannna Wallahi nagaji hakuri ya kare ina dalili gwarama nayi na haihu nabar gidan nan kullum nida yarana bamuda zaman lafiya.
     Bara dan asabe ya shigo nagaya masa yadau mataki.
    Huce kisanya rigar kiyi alwala ankusa sallah magrib.
    Rigar hannun ta tashiga sawa.

Ahankali ta bude idanunta tareda mikewa zaune.kaf idanun ta suka sauka kan Sapna dake tsaye tana saka riga.
     Ya Sapna ina sweet dina da kikace zaki siyomin a makalantan Ku.
    Kai Shaheeda daga tashin ki kya bari mana kici abinci.
    Kanta ta makale jikin kafadarta alamun Aa.
     Kinga karasa saka rigar ki dauko mata inde kin siyo mata dan kinsan halin wannan yarinyar da shegen taurin kai ki dauko mata dan yanzu abincinma saitace baza taciba.
      Daki ta nufa ta dauko mata tareda mika mata.
    Amsa tayi ta duba tareda cilli da ita ta huntsila kan kujerar ta fara kuka.
     Maman tasuce toh uwar rigima menene kuma baga alewar nan ba.
    Mama Wallahi dan tsinken jikinta ne ya fita shine ita wai baza tasha ba.
      Kinga shaheeda ta taso kinji bazamu unguwa da Sapna ba mukadai zamu tafi taho kinji.
      Jiya mata bayama tayi dan bama tasan kallan su kukanta take tsakani da Allah.
    Kinga dauko tsinken inde yana nan ayi dubara inba hakaba Wallahi bazata barmu muyi bacci da ddin raiba.
    Cikin jakar ta shiga dubawa dakyar ta lalubo tsinken ta mikawa Maman taso.
    Danko alawar Sapna ayi dabara ko shinken zai gyaru.
    Alawar data cilla karkashin kujera Sapna ta dauko tare da mikawa Maman tasu.
    Ahankali ta maida tsinkin tayi er dabara ta mika mata.
     Taso ki amsa gashi yanzu tsuntsu ya kawomin ita taho ki amsa karya kwace kayar sa yace ya fasa.
     Tasowa tayi ta matso kusa da Maman tasu ta amsa tareda dubata sosai sannan ta yadda daga gurin tsuntsu take dan akwai tsinke ajikinta.
     Yauwa yarinyar kirki yanzu kawo a ynma baby ta fada tare da nuna cikinta.
     Aa bajan bachiba chima baya bani naci.
   Kai yr kirki yacefa inya zo ke kadaice zaki rinka goyashi kina mai wanka in kika hanashi bazai yanda ki dauke shiba.
     Itade Sapna na zaune tana daure gashinta tana murmushi tana kallan rigimar Shaheeda yarinya karama sai fada.
    Wallahi mama banil bachiba kaya Jo din.kuma nila malin bashi abuna ma ko ya Sapna ta fada tareda maida hannayan ta baya ta langwabe kanta.
     Itade Sapna mikewa tayi ta nufi toilet tareda fadin yanda kikaso.


Bayan sun idar da sallah suna zaune a falo suna kallon cartoon mamansu na cikin daki.
     Dan Asabe ne ya shigo dakin da sallah.
Da gudu Shaheeda ta sakko daga kan kujera ta dane shi ya dagata sama tana dariya.sannan ya zauna tareda dorata kan ciyarshi.
      Yaya kacan  yau ko cuncu ya kawomin alawa daga shama.
    Haba ! Sarkin surutu kin bawa Sapna.
    Zamowa ta danyi daga kan kujerar tareda fadin yaya ina yin,
    Lafiya qlau Sapna ya skul din.
    Lafiya qlau yaya gobe zamu fara exam.
    Gud Allah ya kaimu ya kuma bada sa'a.
      Maman suce ta fito daga dakin sanye da hijab.
    Dan Asabe ne?
    Nine inayini .
Lafiya qlau ya aiki.
   Alhmdullh NA shigo sarkin labari tana bani.
     Wani irin sarkin labari kuma sarkin rigima kai.
     Dariya yayi tareda mika wa Sapna ledar hannun sa.
     Ga ice cream nan aje asha.
     Aikuwa Shaheeda naji ta koce ledar tareda komawa jikin Maman ta boye wai bazatsha ba tunda ta siyo mata alawa maras tsinke.
      Rabu da ita Abu da yanzu zatayi bacci cigaba da kallanki.
    Shima dariyar yayi.sannan yace babu wata matsala ko Aunty.
   Wallahi babu komai saita ya rannan Sapna da safiya na rasa gane Kansu kullum cikin fada yauma sunje sunyi gaba daya ta kwashe littafan Sapna ta watsar kuma gobe zasu fara exam.
      Shiru yayi nadan lokaci sannan yace jeki kira min safiyar.
     Ahankali ta mike ta nufi dakin su safiyar abakin kofa sukaci karo tafito.
     Dallacan ki bani guri mutun sai kace dabba.
    Yaya dan Asabe ke kiranki.
    Bata jira amsar taba ta huce ta koma daki.
   Koda ta dawo bata koma kan kujerar ba kusa da yayan ta zauna tare da fadin gatanan zuwa.
     Da sallama ta shigo sanin yayan nasu na dakin kuma tasan halinsa.
     Jikinta a sanyaye ta zauna kusa da Sapna tareda fadin yaya gani.
       Kallan su yashiga yi na dan lokaci kafin yace bana hanaku fada ba?
    Safiya ce tace Wallahi yaya itace w..
    Zaki min shiru kosainaci mutuncin ki,koma me ta miki ba mutane agidanne da bazaki gaya musu ba zaki zubar mata da lintafanta.
Tashi kije ki dauko mata naki.
     Tsayawa tayi tana kumbure kumbure.
    Ba magana nake miki ba?.
     Yaya bata kwafar note kullum duk note enta incomplete ne.
    Tsaye ta mike tayi baya tana kallonsa Har idanta sun fara ruwa.
    Dama abunda kike kenan a skul din taku,shiyasa kenan kullum kina cikin en last 5.
   Wallahi tallahi zaki gamu dani inde a wannan exam din kika fadi ke ko average kika ci nida kene.
     Sapna kiyi hakuri kinji kuna yin karatun keda frnds dinki ni kadai nasan mezan siya miki wannan karan.
     Mama dake zaune tana bama Shaheeda ice cream Har tayi bcci ajikinta.
     Mama yayima saida safe sannan ya fita daga dakin.
     Itama safiyar fita tayi tana kuka..


❣❣❣❣❣❣❣
Muah........my pple in
 01 Amal fansclub💅🏻🌷


👑👑
Written by Zeenaseer😘
[14/1 12:54] Zeeenaseeer: 🌳🌳.       ⚜.     🌳🌳
🌳.                             🌳
               👑👑

               🌳🌳
                  🌳 
       MARAICHI❣
              NA
 Zainab Naseer Sarki
    (Zeenaseer😘)

0⃣2⃣

Da kuka ta shiga dakin nasu.
    Mahaifiyar ta da suke kira Umma tana zauna tana kallo.tayi maza ta sanya wa kofar ido tana jiran shigowar yar tata da ke kuka.
     Hafsat dake zaune tana Assignment tace Dallah malama waike yaushe zaki kirma saikina barema mutane baki kina kuka saikace ba mace ba.
      Toh kekuma ina ruwanki in bazaki share mata kukan taba ki rabu da ita.
   Wayyo Allah ummana Wallahi bazan yar daba sai de kome za'ae ayi amma Wallahi saina ci uwarta gobe amakaranta.
     Menene uban waye ya tabaki.
    Ba wannan muna fukar yarinyar bace taje ta hadamun karya gurin yaya dan Asabe ita da babanta  Shikuma harda biye musu yayita yimin fada.
     Kede Wallahi munafuka ce kullum saikin hada fada agidan nan banza me kama da biri.
Hafsat ta fada tana hararar safiyar.
     Ummance cikin jin haushi ta nuna ta tareda fadin kece munafuka shakaran banza wanda batasan ciwan yar uwar taba.
In banda ke sokuwace maimakon ki tashi ki shigarma yar uwar taki saikina zaginta.
     Amma Umma kanmi zakina biye mata bayan kisan shegiyar karya gareta.
    Na biye matan.Wallahi Hafsat ki kiyayeni kinji na fada miki.
    Cigaba da rubutunta tayi batare da ta kuma kula suba dan ita harga Allah haushin safiyar take ji.
    Kinga rabu dasu Wallahi karki raga mata inbanda iskanci yarinya kamar aljana,simi simi dakai kamar muna fuka.
Ki kwantar da hankalin ki kishare hawayanki.
Kuma shima Dan Asaban yana munafunci cikin lamarinsa.
     Uhmm Hafsat ta fada ahankali tare da fadin wata rana sai tabaki kunya inde kina biye mata.



👑👑👑👑👑👑👑
     Gidane ha dadde wanda yagaji da tsaruwa,kamar a kasar turai.Gina ya tsaru iya tsaruwa.
     Cikin gidan na shiga dan gaba daya yr kwauye na kuma sabo da kale kale lol😜..
   Ko ina ya tsaru cikin falon na shiga nan nabune baki saboda haduwar sa.
      Wata mata nagani wanda bazata huce shekara 25 fara ce tas kuma tana da jiki ba laifi.zaune take tarkacan takardu a gabanta da alamu making take.
      Salma! Salma!!
Tsaki taja tare da fadin ina zuwa.
    Wai baza'a taba Barin mutun yayi abunda zaiyiba.
Anje pen din hannunta tayi sannan ta mike.
    Cikin dakin shi ta nufa sannan ta tsaya tana kallan sa.
    Kinga shiyasa kullum muke samun matsala dake,kwata kwata kin maida aikin ki yafi komai cikin gidan nan gaskiya bana jin ddi.
     Haba dear! Kaima kasan gobene akesan hada result din yara tunda Hutu za'ae kuma in banyi recording din ba yanxu yaushe kake San nayi.
Kaide kawai baka San aikin nawane shiyasa.
     Aww! Hakama zakice kinan duk hakuri da nake dake dake bakya gani gud kiyi yanda kk so.
     Ta gefanta yabi ya fice dan gaba daya salman haushi take bashi.
     Binshi tayi da gudu tareda tare kofar.
    Ina kuma zaka?
  Inda kika aikeni.
     Amma ai kasan bakamin adalciba baka tashi fita sai kaga wkend ina gida.
    Kibani guri na huce bana San abunda kike yi.
    Wallahi Fahad babu inda zaka je.
   Ahhho! Kina nufin sabo da ke sai naki zuwa gaida iyayena kenan ko?
Meyasa salma kin rainani bakyau ganin gimana nifa mijinkine kidena abunda kk.
    Kabari da yamma kaje ka gaida su.
   Tsayuwa ya gyara tareda fadin inna zauna agidan ki ka gayamin abunda zan miki?
     Kaga fahad kowani ma aikaci yana bukatar Hutu duk wkend saboda haka katafi dakinka kayi kwanciyar ka.inyaso da yamma saika je ka gaida su din.
    Mtewww ture ta yayi tareda ficewa daga gidan.
      Motarshi ya shiga tare da mata key gidansu ya nufa.

Koda ya isa me gadi ne ya bude masa gate din sannan ya park din motar shi.
    Cikin falon ya shiga da sallama. Momi ya na zaune tana duba wani littafi fuskarta dauke da dan karamin glass a fuskarta.
     Zama yayi kan kujera tareda gaida ta.
Littafin ta anje gefe daya tareda cere glass din sannan ta amsa gaisuwar tasa.
Ya gidan ya salma.
    Wallahi duk lafiya qlau ina Aisha.
    Inaga tana sama kirata mana a waya.
Nasan zancan gizo bazai huce na koki ba.
     Wallahi kuwa momi kamar kinsan yinwa nakeji.tazo ta hadamun breakfast.
     Ga wani can da nayima Abban ka yana sauri kadan yaci ya huce Kaduna.
     Yawwa momina Allah ya barmin ke.
    Ameen Allah fahad kana bani mamaki namiji kamar ka bazai iya da gidan saba da anyi magana kace aiki yayi mata yawa ko da kasar take rike at list zata warema mijinta tym dinsa.
     Ba abunta ta iya sai shegen kishin baza.
    Momi Ade mana hakuri za'a gyara insha Allah.
    Kaini bani guri Dallah.
    Mikewa yana dariya ya nufi dinning. Zama yayi yaci abincin ya koshi sannan ya mike ya dawo falon.
     Har yanzu momi tana nan bata tashiba.
   Zama yayi suka dan taba hira kafin yamata sallama ya tafi.

👑👑👑👑👑👑👑
Kwashe gari tunda safe   mama ta tashi tayima su Sapna wanka sannan itama tayi.
     Shiryawa Sapna tayi cikin kayan makaranta ta masu kyau.
Sannan tayi breakfast sannan me daukar su iya iso suka tafi makaranta.

Koda suka iso dama ajinsu daya sapna da safiya.
Primary 5 yellow.
Dama ita Sapna ko a makaranta frnd dinta daya ce Husnah.
Suna zaune suna karatu kafin su fara exam din.
     Gashinta taji anja mata tabaya.
    Ouch! Ta fada tareda juyowa.
    Safiya tagani tsaye itada kawayanta su uku akanta.
    Haba safiya meye hakan zaki jamin gashi ki sakeni mana.
    Dallah malama ki saketa mana ke ko kunya bakyaji gidanku daya amma kina mata Abu kamar ba yar uwarki ba.
      Kinga dakata Husnah bansa dakeba da yr gidanmu nake.
     Mikewa sapna tayi tareda matsawa kusa da Husnah sannan ta kalli safiyar tace ni inajin maganar yayana dan ya hanamu fada sabo da haka kije kiyi tayi.
    Sannan ta kama hannun Husnah sukabar wajan.
    Dada binta tayi ta janyota wannan karin saida ta fadi ta ji ciwo a kafarta.
      Aikuwa Husnah da saurin hannu ta kwada mata mari.
Nan fa dambe ya kaceme aka dinga fada da ker aka rabasu.
    Itade Sapna na gefe kafarta sai faman jini take.
    Nan Auntynsu ta kirayesu dukansu sannan tayi musu hukunci ita kuma Sapna aka wanke mata ciwon nata.
    Haka sukayi exam din Har aka tashesu.
Ko da driver yaxo daukar su dama Sapna ce me shiga gaba dan ita safiya cewa take bazata zauna kusa da itaba.
    Haka suka dawo gida babu wance yayima wata magana .

Da sallama ta shiga dakinsu.jikin mama ta fada tana kuka.
     Lafiya Sapna yau kuma da kuka aka dawo.
    Shaheeda ce itama da idanunta suka ciko da kwalla tace ya sapna waye ya dakeki.
    Cikin kuka tace kalli mama ciwan da safiya taji mini a makaranta.
    Garin yaya kuma ba yynku yace kar kukara fadaba.
     Wallahi bani na jataba kuma banyi fada da itaba.tureni tayi na fadi.
    Wannan wani irin bala'i ne.
    Mikewa tayi da katan cikinta ta kama hannun Sapna shaheeda na biye da ita suka nufi dakin su safiyar.
     Itama tana can ta hada karyarta kuma uwar tata ta yarda tana taa faman fada.
    Sallamar da akayice ta tsaidata.
     Mikewa zaune tayi tareda fadin lafiya maryam zaki shigo min daki.
     Hmmmm Hauwa kenan mezaikaini shigowa dakinki inba kurunin da kuka yiba.
Ke safiya meyasa bakida mutunci
Sapna ba kanwar ki bace amma kika takura mata.yanxu ko wani kika ga yana kokarin dukanta bakya tare mataba.
     Kinga maryam ya isheki haka,ya zaki shigo Har cikin dakin su kina mata fada kamar ke kika haifeta.
    Dole na mata fada kalli kalli abunda tayi mata.ta fada tareda bude mata ciwon da tajima Sapna.
     Bada sukayi kuma aka cuceta kinga kuwa aiba maganar kawo kara.
     Hafsace ta shigo dakin da sallama tana murmushi tareda daukar Shaheeda.
     Aunty dan Allah kuyi hakuri nasan duk akan safiyane.
    Wallahi Hafsat ni kaina rashin jituwar yaran nan yana damuna amma Sam ummanku takasa fahimta Allah ya kauta.
    Dama dole na kasa fahimta,Sapna bata da kunya.
Ke kuma Hafsat zaki gane kiranki sakaran banza.
     Har daki Hafsat ta raka su Sapna sannan ta dawo.
     Tana shigowa dakin Umma ta kwada mata mari.
    Banza mahaukaciya idan na kara ganinkin taka dakin matar can Wallahi saina bata miki rai.
     Amma Umma d.....
Zaki min shiru kosaina kara kwada miki wanda yafi wannan..


😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fansclub💅🏻🌷


Written by Zeenaseer😘
[14/1 12:54] Zeeenaseeer: 🌳🌳        ⚜      🌳🌳                              🌳                             🌳

              👑👑
   
             🌳🌳
               🌳
    MARAICHI❣
              NA
 Zainab Naseer Sarki
     (Zeenaseer😘)


0⃣3⃣

Safiya ta gallama harara tareda shigewa cikin daki.

Zama tayi kan kujera Shaheeda na gefanta,
Har yanzu gurin yana miki ciwo Sapna?
    Eh amma ba sosai ba kuma na gayama Auntyn mu ta dau mataki.
     Allah ya kyauta muje ki canza kayanki kice abinci kutafi islamiya.
    Ya Sapna nima zani makalantan kinji mama kice taje dani tana magana tana dukan ciyar Maman tasu.
     Toh zataje dake dan Allah haba sai damun mutane kinasan kije makarantan kuma inkinje din kiyata dukan yayan mutane.
   Baya taja tajuya tareda zama akasa tana kuka harda hawaye.
     Sapna ce ta matsa kusa da ita tareda fa tsugunnawa.
     Haba my cwt sis dake zan tafi rabu da mama bazamu bata abun muba.share mata hawayan tayi tareda rungume ta.
     Ita kanta mama yaran nata NA burgeta burin ta arayuwata su samu rayuwa me kyau shiyasa koda yaushe take musu addu'a.
    Tashi mana Sapna kije ki dauraye jikinki ga kayan makaranta can na dauko miki.
    Mikewa tayi tareda rike wannun Shaheeda suka nufi daki.
    Sunata wasa da dariya harta gama shiryawaabinci suka zauna sunaci suna bawa juna abaki Har suka gama.
    Hajib dinta mama ta sanya mata tareda basu kudin makaranta.
Hannun Shaheeda Sapna ta kama suka fito.
    Da kamar ta shiga dakin su safiya tace ta taho su tafi makaranta amma sai tayi tunanin abunda zai biyo baya.
    Tafiya kawai sukayi Har suka karasa makaranta.

👑👑👑👑👑👑👑
Tana zaune cikin falon ta taji sallama da sauri ta dago da kanta.
    Zuby ce kawara ta.
Da sauri ta mike tsaye tareda fadin haba zuby sau nawa kike San nagaya miki bana kaunar kawata ko daya ta dunga zuwamin gida.na ce duk lokacin da kksan ganina ki fadamin dan akan mijina babu abunda bazan iyaba.
    Gaskiya salma baki da hankalin. Kenan duk inda fahad din zaije kina tare dashi ko.ki angaya miki namiji ana hanashi San Abu ne.
    Da sauri tayi kukan kura ta shaki huyan zuby tana fadin karya kike fahad bazai taba San wata mace a duniya ba bayan ni.
    Da ker ta kwaci huyanta daga hannun salma tareda komawa gafe tana tari.
Karya kike mahaukaciya kuma insha Allah sai fahad yayi miki kishiya.
     Ke ni kike gayawa wannan maganar.
Nan suka hau fada doke doke fada sosai.
 
Fahad dake kwance cikin daki yaji karar hayaniya.
Da sauri ya fito falon ganin kome ke faruwa.
     Aa aa salma menene haka kukeyi.
    Sai lokacin salma ta saki zuby.
   Nan ita kuma zuby ta fashe da wani saban kuka na kissa.
     Kinga ni ko salma zaki kashe musu yarinya ko,ba gurinki tazo bane.
     Kallan shi take tanata faman huci tareda fadin.fahad ka koma ciki dan Allah zan bata hakuri ta tafi.
    Tsaki yayi tareda yin gurin zuby yaga me takema kuka.
     Janyoshi tayi tareda fadin ina ruwanka da ita kuma gaskiya fahad ka bari.
    Zaki bani guri kokuwa.
    Wallahi kome zakayi saide kayi amma bazaka gurin taba.
    Kanta yayi Har zuwa daki tareda kulle ta yasama kofar key.
    Kamar zata yi hauka tahau buga kofar cikin haushi tana kwalama Fahad din kira.
    Amma yayi banza da ita tareda barin wajan.
    Dan kwalin kanta ta cire tare da wargar dashi ta kama yawo acikin dakin tana hargitsa gashin kanta kamar mahaukaciya.
Duk da sanyin Ac amma ita gumi take saboda bala'in kishinta.
     Shikuwa wajan zuby ya karasa tareda fadin lafiya da ko pls kiyi hakuri Wallahi narasa abunda ke damun ta kiyi hakuri pls.
     Babu komai fahad Amma ya kamata ka gaya mata ta rage abunda takeyi dan wata rana zai kaita ga halaka.
   Sannan ta mike tareda daukar Vail da bag dinta tabar gidan.
      Zama yayi agurin tare da kama kanshi tabbas salma batada hankali yakamata yadau mataki akanta dan wata rana zata jamasa abunda yafi karfinsa.
     Mikewa yayi tareda zuwa ya budeta.
    Da sauri ta mike tareda biyo shi jikinta duk tayi ja.
    Dakata Fahad me ka gaya mata.
Bai kula taba yaci gaba da tafiya.
   Magana fa nakema Fahad ka shareni .
   Kinyima yarinya duka ta kasa tafiya shiyasa na dauketa na kaita motarta.
    Jiki tayanke ta fadi.
Juyowa yayi ya ganta asume.
    Jikinsa na bari ya dauketa ya maida ta kan kujera tareda debo ruwa ya watsa mata.
    Ahankali ta bude idanunta suka hada ido dashi.
Sabn kuka ta fashe dashi.
    Da gaske ka dauki zuby Fahad.
   Dariya taso bashi amma ya dake.
    Menene danna dauketa bake kika jaba.
    Amma meyasa kake min irin wannan pls habibee.
  Am sowie bby ke kikaja banasan irin wannan kishin naki kirage zai iya illataki.
    Rungume shi tashi tareda fadin insha Allah ka tayani da addu'a pls bby.
    Kara matseta yayi ajikinsa anamiki koda yaushe.
    Rufe idonta tayi tanajin irin son da takema Fahad din dan akanshi zata iya kashe mutun kuma ta kashe kanta.🙄

👑👑👑👑👑👑👑
  Bayan sunje makaranta an taso ne suna cikin tafiya wata yr makarantar su ta biyo mayanta rike da kanwarta.
     Ke Sapna tsaya Wallahi ki yima wannan kawar taki magana kalli yanda ta fasama kanwata hannu saboda cizan da tayi mata.
    Kallan Shaheeda tayi da alamar tuhuma.
    Ya Sapna itafa ta fara tsokana ta kuma ta cijeni nima.
     Dan Allah kiyi hakuri bazan karama zuwa da ita makarntar ba.
Sannan ta dafawa yarinyar da aka ciza kanta tareda fadin yakuri kinji kanwata zan rama miki.
   Sannan suka tafi itama hanyar gida suka nufa tana fadin zaki gane ban kara zuwa dake tunda kika ciji yr mutane.
     Ya Sapna Wallahi nima duk wanda ya doceni saina lama.
   Chof! Uwar tsokana kawai.
    Da sallama suka shigo gidan kasan cewar haka mamansu ta koya musu babu kowa atsakar gidan dan haka dakinsuka shiga tareda cire hijab dinsu.
      Mamansu suka shiga kira amma shiru basu jiyaba Har bandaki suka duba nan Shaheeda ta kama kuka mama ta tafi unguwa ta barmu ya Sapna.
    Ya kuri kinji bata tafiba rungume ta tayi dan itama bataji dadin rashin ganin Maman tasu gashi tana tsoran wanda zata tambaya.
      Zani ta dauko ta goya Shaheeda data fara jin bacci dan anjima da kiran magriba.
     Dakinsu safiya ta nufa da sallama amma bakowa a falon.
Saboda tsoro kasa shiga falon tayi daganan bakin kofar ta tsaya tana jirana fitowar wani.
    Ummace ta fito daga dakin ganin Sapna tsaye da goyo tace lafiya zakixo ki tsayawa mutanen anan wajan.
     Idonta na hawaye murya na rawa tace dama ma.....m..mam mu nake nema.
   Dallacan fita kiba mutane waje.
   Jiki asanyaye tana goge hawayan nata tafito waje.
    Sapna kukanme kike Hafsat ta fada tana kokarin shiga dakin.
   Dama mamanmu nake nema.
   Haba Sapna sai kace baki da waye.to mamanku tana asibiti zata Haifa muku dan baby.dazu Anty Naja ta dauketa suka nufi asibitin kibar kuka muje ki zauna.
     Ba musu suka koma cikin dakin.
   Umma dake zaune kan kujera tana ganin sun kuma dawowa tace ubanme ya kuma dawo daku.
    Sapna kallon Hafsat take taji me zatace.
   Umma gani nayi mamansu bata nan kuma kinga ba ddi abarsu sukadai tunda yarane.
    Dallacan ina ruwana abar sun mana.kufita Ku bani waje.
     Sapna da Har lokacin kuka take goyeda Shaheeda a bayanta.
Juyawa tayi zata fita Hafsat ta kamu hannunta tareda fadin muje na tayaku kwana.
    Dawo nan ba inda zaki tunda naga baki da hankali bakya  kishin uwarki.
    Umma amma da yaran zanyi kishi.
   Dan uwarki inni na haifeki kuma na isa dake ki huce ki shige .
Kukuma munafukai kubarmin daki.
Hafsat kasa matsawa tayi daga gurin.
Tana ganin Sapna ta fita daga dakin tana kuka.
Kamar tayi kukan haka ta Ruga dakin.
    Sapna ga tsoro fal cikin rainta ga yunwar da takeji.
Haka ta bude dakin nasu ta shige ahankali ta sauke Shaheeda daga bayanta.
   Tashi tayi tareda matsowa jikin sapnar idanta rufe tace mama!
    Wani kukane ya kuma kwace mata da sauri ta toshe bakinta takuma rungume yar uwar tata.


😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fansclub💅🏻🌷


Written by Zeenaseer😘
[14/1 12:54] Zeeenaseeer: 🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
        MARAICHI❣
                NA
  Zainab Naseer Sarki
      (Zeenaseer😘)

0⃣4⃣
ASALI☃

Alhaji Ibrahim Sunusi haifanfan garin kebbi state ne, mutun ne mai mutunci da Sanin ya kamata.yana da ilimin boko dana mahammadiya daidai gwargwado.
    Bayan ya gama karatunsa saiya fara kasuwancin sa nan garin kebbi.Allah ya samai hannu cikin sana'ar tasa ta saida kayan masarufi.nan ya bude katan shagwansa na saida kayan abinci.kuma alhmdullh yana ciniki sosai.
      Nan Allah ya hadashi da mace mai mutunci hankali da nutsuwa wato Rabi'at.bayan sunyi aure da shekara daya da rabi Allah ya basu haihuwar yar mace nan suka samata suna Maria sunan mahaifiyar sa,suke kiranta da Ummi.
     Saida mariya ta shekara 5 sannan Rabi ta kuma haihuwa da namiji nan suka sami suna Aliyu da yake ranar assabr aka haifesa sai suke kiransa da dan Asabe.
      Bayan dan Asabe yayi shekara 3.Alh.Ibrahim ya karo aure hauwa'u.
Rabi bata nuna damuwar ta ba kan auran da mijin nata ya kara.ita kuwa Hauwa ganin Rabi ta fita kyau ga hankali yasanya ta tsaneta kuma koda yaushe cikin janta fada take ko takama yaranta tana duka.
    Hakan yana mugun batama Rabi rai Amma saitayi shiru bata magana.saima ta hana yaranta fitowa kullum suna daki dan batasan tashin hankali.
    Gashi in ranar girkin tane bata gama abinci da huri yara suyita faman jin yinwa saide ta sama musu abinda zasuci.
    Koda ta sanarwa mai gidan nasu saiyace sai anayi ana hakuri ba sabawa tayi ba.
    Taji haushi sosai Amma saita daure.
    Shekara Hauwa daya da zuwa itama ta haifi yrta mace mai suka saka mata Halimatussadiya.
    Yarinya ta tashi cikin gata dajin dadi.
   Nan mai gidan nasu ya fara nuna banbanci dan yafi kaunar Sadiya kan sauran yaran nasa.
    Hakan bayama Rabi dadi amma saitaci gaba da hakuri watrana sai labari.
     Shekarar halima 2 ta kuma haihuwa amma itama wannan karan namiji ta Haifa.
    Tayi murna sosai dan gani take kamar sun zama kai daya da Rabi.
     Ana gobe suna Allah yayima yaro mutuwa.
     Nanfa hankalin Hauwa ya tashi kamar zatayi hauka Allah ya kasheta Rabi ce takashe mata danta.
    Itade rabi vanda kuka ba abunda suke ita da yaranta,haka suka hadu da danjinta suka rinka cewa ai mayyace ita tanaji kamar ta mutu dan bakin ciki Amma haka ta hakura ta shige dakinta.
    Tun daga wannan rana gaba mai tsanani da tsana ya kuma shiga tsakanin Rabi da Hauwa.
    Amma ita Rabi bataji ddin hakanba dande bayanda ta iya.
   
Yana shekara daya da mutuwar dan gidan Hauwa ta kuma haihuwar da namiji.murna ba'a magana.
Sai fana habaici take kamar ita taba kanta haihuwar kuma ta hana ta daukar dan karta kashe mata shi.
     Nan aka sama yaro Aminu suke ce masa Abba.
    Sun nunamai gata hakan yasa yaran yataso bashi da kunya ko kadan dan Har iyayan nasa baya ganin girmansu.
      Hakanne ya fara damun Alh. Ibrahim dan bayasan yara maras sajin magana tun yana dukansa haryama gaji ya rabu dashi.
     Bayan shekara 6 da haihuwar Abba.Rabi takuma haihuwar yarta mace.taji dadi sosai kuma tayi farin ciki,ranar suna yarinya taci Khadija amma Nana suka ce mata.
    Yarinya fara tas kyakyawa dan tafi kowa kyau agidan nan Ummi tasamu kanwa kullum tana goye da ita tana mata wasa.
      Haka rayuwa taci gaba gidan Alh. Ibrahim suna samun kulawa me kyau wajan baban nasu.dan babu abunda baya musu dan suji ddi.
    Yasanyasu amakaranta suna karatu tukuru.
    Shekarar Nana 2 ,Hauwa ta kuma haihuwar yrta mace itama aka sanya mata Hafsat.
    Tunda ga kanta babu wanda yakuma haihuwa acikin gidan Har lokacin da aka yima Maria Aure.
     Ta auri wani mai rufin asiri kuma saurayi Amma shi dan katsinane.
Nan suka kaita katsina.
Mutukar haushi Hauwa tana jinshi nan tasa Sadiya akan itama taso mu mai arziki ayi mata auran.
     Bayn andan kwana biyu da bikin Maria itama Sadiya takawo wani Alhaji mai kudi tace shitake so a aura mata.
     Hauwa taji ddi sosai nan tasa akayi mata auran itama Ashe yana da mata biyu itace ta uku.nan juwa aka kaita dande kowa part dinshi daban.
     Gidan ya rage daga dn Asabe sai Abba, Nana da Hafsat.

 Nana da Hafsat sun taso kamar yn biyu kasan cewar Nana bata da girman jiki sai kuka zama kusan kai daya da Hafsat.
    Duk da in suna gida Hauwa bata barinsu zama guri daya.Amma amakaranta suna tare sunyi mutukar shakuwa da juna.
     Komai tare sukeyinsa.ko dayace taga daya ta sanya kaya to itama irinsu zata saka.
Hakan yana yima Rabi ddi kuma dukansu ta dauke su amatsayi yayanta.
     Dan Asabe ma ya dage yanata karatu kuma alhmdullh yana da kokari sosai kuma yana dan zuwa kasuwar baban nasu.
     Shikuwa Abba irin yn isakn samarinnan ne.kullum yana gabtali baya zama agida.ga shegen San mata ga shaye shaye.
    Kuma ga shegiyar sata dn ko Babar shice ta anje Abu yana gani zai dauke Amma ita ko ajikinta dan ita ke kara daure masa gindi yayi abunda yaga dama.

     Alh.Ibrahim ya gina musu saban gida mekyau kowacce daki ciki da rumfa Har nashi.
   Nan fa ya cancado sabuwar Amarya maryam kyakyawa jajir da ita yr garin bauchi ce sunzo sunan yayarta data haihuwa nan ya ganta kuma itama ta amince akasha biki.
     Hauwa taji haushi sosai kishi kamar ya kasheta dan mugun haushin maryam din takeji.
     Kyakyawa da ita ga hankali, ilimi da nutsuwa.
Hakan yasa suka hade kansu da Rabi hankali kwance dan yayama take kiranta.
     Bata jima da zuwaba ta samu ciki dama itama Hauwa tasamu cikin amma saita Riga maryam din haihuwa.
     Wata rana Hauwa ta sanya Abba yayima maryam duka gashi lokacin cikinta ya fara tsufa.
    Tasha wahala sosai kamar zata mutu nan Alh. Ibrahim ya kori Abban daga gidan yakuma fada ya cireshi daga cikin yayansa.
     Nan Hauwa ta dunga hauka wai antsaneta tunda aka kori danta.
Haka tayi ta gama.
     Bayan kwana biyu ta haifi yarta safiya.itakuma itace mun muna acikin gidan.Amma haka Hauwa ta dauki San duniya ta Dora kan Safiya shiyasa itama ta tashi da hali irinna uwata.
     Bayan wata hudu da haihuwar Safiya itama maryam ta haihuwa aka sama yarinya Sapna. Ansha shagali sosai dayake danginta suna da kudi.
     Yarinya ta tashi cikin soda kauna gurin yanyanta kullum in bata bayan Hafsat tana gurin Nana dayake sun saba sosai dasu.
     Abunda ke hadata da uwanta bcci dashan nono.
   Haka itama taji ddi sosai.

Shekara ta biyar ta kuma haihuwa mace aka sanya mata Fatima suke kiranta Shaheeda da yake sunan mamantane.
    Haka rayuwar gidan taci gaba da gudana.
    Maria itama yaranta biyu ita kuwa Sadiya bata taba haihuwa ba.

 BAYAN SHEKARA 2
RANAR TALATA.
    Allah yayima Alh. Ibrahim rasuwa babu ciwo ko dan kawai wayar gari akayi babu shi.
    Kowa yaji mutuwar nan sosai abun tausayi lokacin maryam Nada karamin ciki.
    Gida kullum cike yake da yan uwa da abokan arziki anata amsar ta'aziya.
     Haka yara kowa yayi kukan rashin babansa.Har Shaheeda da take karama ganin ana kuka itama takeyi.
    Haka akaita zaman makoki Har tsawan kwana 7.sannan kowa ya kama gabansa.
     Nan fa Hauwa ta fara tunanin yanda zata raba maryam da Rabi subar gidan.
   Haka kuwa akayi nan tashiga ta fita tayi musu asiri itade maryam bai fara aiki akantaba.
     Amma Rabi hauka tafara tuburan.nan hankalin yaranta danasu maryam ya tashi suka shiga nemamata magani abun abun tausayi dan duk wanda ya ganta saiya tausaya mata.
    Nan suka dauketa suka kaita gidan mahaukata.satinta uku a can aka aiko musu cewar ta kashe kanta.
     Hankalin kowa yayi mugun tashi nan itama aka maidota gida akayi jana'iza.sunyi kukan rashinta sosai.
      Bayan sadakar bakwai maria tace zata tafi da Nana ta zauna agurin ta Har zuwa auranta.
     Amma rasuna kawo musu ziyara.maryam da Hafsat sunyi kukan rashin Nana sosai dan tan kaunarsu itama haka suka tafi suna kukan rabuwa da juna.
     Haka rayuwa taci gaba in ansamu Hutu Nana kanzo ta jima dakin maryam take sauka.
     Kuma dan Asabe ke kula da gidan duk abunda sukeso shiyake musu amma Hauwa da suke kira Umma bata gani.
    Haka kuma danta Abba ya dawo gida Amma shi baya yawan zama agida kullum yana gantalin sa.

Su Hafsat suna level 200 ita da Nana kuma suna yawan waya.Amma Umma bata taba barinta taje katsinan ba.
     Sapna da Safiya kuwa suna primary 5 yanzu ne zasu shiga jss1.
    Shaheeda ce kawai bata shiga makaranta ba.
 
Ynxu dan Asabe zai gyara gidan saboda aure zaiyi ya mai dashi part biyu danashi Dana sauran matan.
     WANNAN KENAN😉

😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fansclub💅🏻🌷


Written by Zeenaseer😘
[14/1 12:54] Zeeenaseeer: 🌳🌳       ⚜       🌳🌳
🌳                             🌳
              👑👑
                🌳
     MARAICHI❣
            NA
 Zainab Naseer Sarki
    (Zeenaseer😘)


0⃣5⃣

Kara rungume ta tayi a jikinta tana hawaye, ga wani masifaffan tsoro datake ji.yanxu in Shaheeda ta tashi ya zatayi da ita gata da shegiyar rigima.
    Wata iriyar yunwa take ji.
Ahankali ta kwantar da ita dan karta tashi.
Cikin daki ta nufa ta duba dan basket din da mama ke anje kayan ciye ciye sabo da Shaheeda. Cikin sa'a kuwa yasamu biscuits, chocolate da juice na jarka.
    Biscuit ta dauka da juice guda daya ta cinye.sannan ta shiga toilet tayi alwala dan ta riga ta saba sai tayi sallar ishsha kumin dare,ko tayi bacci sai ta tasheta tayi.
     Saida tayi sallah ta idar.sannan ta kama addu'a Allah ya sauki mamansu lafiya ya basu yar bby.
    Sannan ta mike ta kulle dakin.dawowa tayi ta dauki Shaheeda ta shiga daki da ita ta kwantar.
     Tana ta faman lallabata karta tashi Amma saida ta tashi dan yinwa take ji itama.
Zaune ta mike akan gadon tana murza ido tana kiran sunan Maman nata.
    Sapna dake zaune tana kallan ta tama rasa abinda zatace mata dan inhar tasan Maman batanan akwai bala'i.
    Dabarace ta fado mata ta maza ta dauko mata biscuit da juice ta bude mata tare da fadin Heedah ta maza ki ci ki shanye mama tana toilet inta fito bazata baki ba.
     Idanta arufe ta jingina da jikin Sapna, tana samata abaki tana bata juice din tana sha harta shanye.
     Sannan tayi shiru ajikin Sapna tana fadin mama!!!
    Itade Sapna sai shafa mata baya take ahankali yanda bazata tashiba.
Har taji ta dena abbatar sunan Maman tata.
    Anjiyar zuciya tayi tareda kwantar da ita,ta rungume ta tayi musu addu'a tareda rufesu da bargo.
    Tabbas tana tunanin bazata iya bacciba dan bata saba kwana su kadai ba.
     Hawaye ne ya rinka rubo mata ta gefan ido mayesa mama bata tafi dasu ba gaskiya tsoro takeji.
     Mikewa tayi ta dauki Shaheeda ta kuma goyata sannan ta fito daga cikin dakin ta kuma komawa dakin Umma.
    Wannan karan bata shigaba saita tsaya abakin kofa tana kuka kasa kasa.
      Babu kowa cikin falon dan Umma ta jima dayin bacci.
     Hafsat ce take waya,kara jin kuka yasan yata lekowa.
    Sapna ta gani tsaye ta hada kanta da bangon dakin tana kuka.
    Ahankali ta karaso wajansu kamar tayi musu kuka tace!
   Sapna bazaku iya kwana Ku kadai ba ko,yanzu gashi dare yayi Dana kaiki gidan Aunty Naja (yayar mamansu).
   Amma kinga shigo mu kwana tare daku afalo tunda Umma bata tashi da asbah saiku koma da kinku kinji.
    Shigowa tayi tana goge idanunta Har sunyi ja.
   Sauko Shaheeda tayi daga bayanta Hafsat ta amsheta tareda kwantar da ita kan kujera sannan ta nunawa Sapna three sitters ta kwanta.
Daki ta shiga ta dauko blanket ta lullubesu.sannan ta janyo katifa tsakiyar falon ta shimfida itama ta lullube.
     Harta kwanta Shaheeda tace ya Hafsat ki maido Shaheeda kusa daki sabo da tana farkawa amma kinga inta farka taji da mutun kusa da ita baxatayi kukan ba.
    Murmushi tayi tareda dau kota ta maido kusa da ita.
     Sannan ta rufesu tareda yin addu'a.
 Sai lokacin hankalin sapna ya kwanta amma Har yanzu tana tunanin rashin Maman tasu.

⚜⚜4:00am⚜⚜
    Lokacin Hafsat ta farka dan bacci rabi da rabi tayi dankar Umma ta farka ta koresu cikin dare.
     Tana mikewa lokacin duk basu farkaba.ahankali ta dauki Sapna ta nufi dakinsu ta kwantar da ita kan gado.dan batasan ta farka.sannan ta koma ta dauko Shaheeda ta maidota kusa da ita sannan ta fita daga dakin.
     Tun lokacin da Hafsat ta dauko Sapna ta farka shiru kawai tayi dan batasan damun hafsar.
Matsuwa tayi tareda kuma rungume kanwar tata.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
Ita kuwa mamansu bayan tafiyar su makaranta ta farajin kanta yana Sara mata hakanne ya sanyata kwanciya tadan huta Amma tun daganan ta fita haiyacinta ta dinga birgima akasa ga ciki ajikinta tamkar mahaukaciya.
     Dan kwalin kanta ta cire tare da fito ahaka.
    Hafsat na tsakar gida tana aiki taga ta fito tayi hanyar waje.
Da sauri ta kaomota tareda fadin lafiya Aunty ko nakudarne bara na kira miki Aunty Naja dan ita tasan bazata fara tunkaraa ummantaba yanzuma tasan wanka take data fito ta fara fada.
     Itade maryam idanta arufe sai wasu irin maganganu take.
    Daker tasamu ta turata cikin daki sannan ta kullo.
Hijab dinta ta sanya sannan ta nufi gidan Aunty Naja.
Da sallama ta shiga gidan da yake yaranta maza guda biyu koma duk basa nan.
     Falon ta shiga hankalinta atashe.
Itama fitowa tayi daga daki danjin sallamar da daketa faman yi.
    Aww! Hafsat ce lafiya na ganki ahaka.
   Wallahi ba lafiya ba ni bansaniba Aunty maryam nakuda take kokuma nide dan Allah kizo kiba yanda take Allah abun tausayi.
     Innalillahi Wa'inna ilaihir raji'un.
Dama saida akace ta tafi gida ta haihu ita uwar San yaya tace yaranta ga kuma makarantar su.
     Bara na dauko hijab dina muje.
    Daki ta shiga ta sanya hijab dinta ta dau key din motar ta sannan tace da Hafsat muje ko.
      Cikin motar ta suka shiga nan danan suka isa kofar gida.
      Daker ta iya parking dan hankalin ta duk atashe yake.
Cikin gidan suka shiga kai tsaye dakinta suka nufa Hafsat ta bude sannan suka shiga.
Kwance suka ganta akasa duk ta ji ciwo a kanta.
     Hafsat pls kamamin ita mu fita musata amota.
    Da yake Aunty Najar tana da dan jiki.
Nan suka fito da ita Har sunkai bakin kofa.
    Dakata Umma ta fada cak suka tsaya.
Gidan ubanwa zakije dawo nan.
    Tsaki Najar taja tareda  ciccibar Maryam din tayi waje da ita cikin mota tasaka ta.sannan ta shiga side din driver ta fiji motar zuwa cikin asibitin.
      Amma Umma gaskiya ke rage kiyaryar da kikema su Aunty maryam dan bakisan inda rana zata fadi ba.
     Agidan ubanki zata fadi sakaran banza marar kunya.Anya kuwa kina da hankali,
Dande agida na haufeki da asibiti ne cewa zanyi canje akamin.
      Kamar zatayi kuka ta shige daki.
   Aikin banza aikin hofi wayake da asara inta mutu harda za'a rinka rawar jiki akanta.
Tsaki taja ta koma cikin dakinta.


Suna isa asibitin aka huce da ita emergency nan suka shiga duba.
   Bayan mintina kadan likitan ya fito sannan ya samu Naja ya sanar mata ta farka kuka tana dakuda Amma insha Allah nan bada jimawaba zata sauka lafiya.
Allah yasa doctor nagode.
    Nan ta zauna tanata addu'a wayarta ta dauka ta kira gida bauchi ta sanar musu nan suka hau yimata addu'a suma.dan suna tausaya mata.
   
   Bayan mintina goma wata nurse ta fito hannun ta rike da jariri ta karsu tareda fadin kune kuka kawo wata me ciki.
     Jikinta na rawa tana daga kai tace eh mune.
    Mika mata yaranta tayi .
    Da sauri ta amshe shi tana hawaye tana murmushi.yaro kyakyawa fari tas kamar mamanshi.
     Hajiya ammafa saide kiyi hakuri yaron barai yazo.
     Da sauri ta dago kanta tana kallan nurse idanta yayi jajar hawaye na diga kan fuskar bbyn.
Kasa tsayawa tayi taja da baya ta zauna tareda rungume shi a kirjinta tana kuka.
      Tabbas yanzu taga yaran Amma tajisanshi Har cikin ranta kuma taji mutuwar shi.
Kuka sosai takeyi.
     Ita kanta nurse din taji tausayinta.
Hajiya hakuri zakiyi duk mairai mamacine.
    Dagowa tayi da jajayan idanunta ta kalli nurse tareda fadin ita kuma uwar yaran fa.
Ta karashe maganar wani hawayen na dda bin fuskar ta😭...


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fansclub💅🏻🌷


Written by Zeenaseer😘
[14/1 12:54] Zeeenaseeer: 🌳🌳       ⚜        🌳🌳
🌳                              🌳
              👑👑
                 🌳
      MARAICHI❣
               NA
 Zainab Naseer Sarki
     (Zeenaseer😘)


0⃣6⃣

Gaskiya dangane da matsalar haihuwa babu amma de kije likita nasan ganinki.
    Jikinta na rawa tabi bayan nurse din har office din likitan sannan ta yimata iso da tashiga ita kuma ta kuma.
     Har lokacin yaran na rungume ajikinta tana hawaye.
Sallama tayi tareda shiga kafor ta tura sannan ta nemi guri ta zauna tana goge fuskar ta.
    Kallan ta yayi tareda zare karamin glass din dake idan sa.
Hajiya saide kuyi hakuri dama Allah yayi yaro bazeshaki iskar duniya ba.
    Kanta kawai take iya gyadawa dan gaba daya tashiga damuwa jitake kamar danta tarasa.
     Yawwa sannan dama inasan sanar dake ko kuma ince inasan tambayarki.
Daman matar da kuka kawo tana da wata matsalane a kwakalwa ko iska dade wani Abu makamancin hakan.
    Kai ta gyadamai alamun Aa, tana kallan sa.
    Toh gaskiya hajiya matar da kuka kawo bata da lafiya ameen tanada matsala a kwakwalwarta dan daker muka samo kanta wajan haihuwar nan.
   Gaskiya doctor lafiyarta kalau kuma bata da matsalar kwakwalwa saide wajan nakudar nan tasmeta.amma ayi mata x-ray agani ko tasamu matsalar.
    Shikenan ba matsala tana dakin Hutu dan munyi mata allurar bacci kuma ina ganin sainan da 10hrs zata farka.
    Toh likita na gode Allah yasaka da alkhair
   Ameen babu komai Allah ya jikan yaro.
   Ameen thumma ameen tafada tareda mikewa tabar dakin.
    Dakin da maryam take ta nufa tana hawaye yaran sabe akafadarta.koda tashiga tareda sallama dakin shiru ita kadai kwance tana faman bacci sun canza mata kaya.
Zama tayi kusa da gadan tana kallanta.lokaci daya harta canza ta kara wani irin fari fuskar tayi fayau.
    Ahankali takai hannunta ta shafo gashin kanta Har zuwa fuskar ta.
Lokaci daya ta tuna dasu Shaheeda hankali ya kuma tashi batasan lokacin da saban kuka ya kuma kwace mataba.
     Wayata ta dauka tareda kiran gida ta sanar musu da abunda ya kuma faruwa.
   Hankalin kowa ya gama tashi dan suna kaunar maryam din itace Auta acikin gidan.nan suka sanar da Naja insha Allah gobe suna kan hanya.
    Nan ta kuma kiran dan Asabe ta sanar masa.shima hankalin shi ya tashi sosai nan danan yawo asibitin dan ya tausaya mata.

Bai wani dau lokaciba ya iso dan gaba daya baiji dadin hakanba.
    Dakin yabturo da sallama bayan sun gaisa da naja ta mika masa yaran.
   Kallan yaran yashigayi kamar yayi kuka dan yabtausaya mata.
Ahankali yace yanzu bara naje da yaran nan ayi masa sutura akaishi tunada kinga yanzu kamar dare ya fara.
   Shikenan ba damuwa nima bara naje gida dan zan dauko wasu an kaya tunda kaga kwana ya kamani.
    Tare suka fito daga asibitin kowannan su yayi cikin motar sa.

Tana zuwa gida daukar duk abunda zatayi tayi sannan ta fice daga gidan.


Shikuwa Dan Asabe gidan liman din layinsu yakai yaran aka mai wanka aka shirya shi sannan suka kaishi.
   Asibitin ya dawo shima ya zauna sai dare sannan ya dawo koda ya kuma gidan tunanin su Sapna yake ko sunci abinci koya zasuji.dan yasan Umma ba ruwan ta sai kuma ya tuna ai Hafsat nan.kuda yataso zaije ya dubasu sai yaga Har sun kulle gidan hakanan ya koma ya kwanta.Amma tabbas yana tausayama yarana.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
Har gari ya fara haske amma Sapna bata koma baccin ba.
    Ahankali ta sauko daga saman gadan ta nufi toilet alwala toyo sannan tayi sallah.
Zama tayi kan abin sallah tareda fashewa da kuka sosai take kukan sannan ta fara fadin.
   Allah ka dawo mana da Maman mu kasa bata mutuba,Allah kasa mama bata mutuba ta dawo mu rinka zama tare.
    Ma..mahh! Shaheeda ta fada tareda mikewa ta zauna.
   Da sauri Sapna ta goge hawayen idanta tareda hawa kan gadan.
Ta kankameta tana hawayan.
    Ya Sapna ina mama?
Shaheeda kiyi bacci mana ko kinasan dodo ya kamaki.
    Girgiza kanta tayi tareda kara shigewa jikin sapnar tana Ajjiyar zuciya jin an amabaci dodo.
    Ahankali tace ya Sapna toh kar dodo ya cinye mama.
    Bazai ciye taba kiyi shiru in kika kara magana zaizo ya kamaki.
    Kara rufe ido tayi tareda kuma matsewa jikin Sapna.

Tsawan lokaci suna manne da juna.
So take taje tayi wanka ta shirya dan tafiya makaranta.
    Shaheeda! Ta ambaci sunan Ahankali
  Uhmm! Tace.
Bakiyi baccin bah?
   Ya Sapna ni natashi bana jin bacci.
  Toh taso muje muyi shower kinji.
    Toh ai dodo zai kama mu.
   Taso bayanan ai na koreshi.
   Kamo hannunta tayi tareda saukowa daga kan gadan.
   Ya Sapna ina mamana take?
    Bara muyi wanka saina kaiki wajanta ko yn kirki.
   Kai ta daga tana dariya.

Toilet din suka shiga dayake ko ina da hasken huta.
   Kayanta ta cire sannan ta cirema Shaheeda nata.
    Shower ta kunna nan Shaheeda ta fara tsalle cikin ruwa tana dariya.
   Itama biye mata tayi sunata wasa da dariya Har tayi wankanta ta gama sannan yima Shaheeda.
    Towel ta daura sannan ta daurama Shaheeda nata da mama ke mata amfani dashi.
    Nanma da wasa da dariya tayi mata shafa sannan ta sanya mata kaya.
    Itama shiryawa tayi cikin uniform dinta tsaf ta fito.
    Tana cikin saka sos dinta Shaheeda ta kuma fitowa daga daki fuskarta kamar zatayi kuka tana kiran mama dan ta fara gajiya da rashin ganinta.
    Da sauri ta taso tana kiyi shiru muje in kaiki.
   Amma ina hakurinta ya kare dan tsalleta fara tana kuka.kamar Sapna tayi hauka haka ta koma,dan tasan tabbas ta kama wannan kukan nata kafin tayi shiru sai anyi da gaske.
     Kumawa tayi ta zauna ta barta tanata kukan Har tagama shiryawa.
   

Wayarshi ya dauko tare da kiran Hafsat bata jima tana ringing ba ta dauka tare da gaidashi.
     Yauwa taho ki bude gidan mana lokaci yana kurewa kuma dayara daza'a kai mkrnta.
   Tam.tace tareda kashe wayar ta fito ta bude mai gidan sannan ya shigo.
     Inasu Sapna ya tambayeta?
    Suna dakin su.
Kina nufin su kadai suka kwana.
    Habade yaya bade su kadaiba dakin Umma suka kwana dazu na mai dasu daki.
    Ohk kin kyauta Amma Aida kin shiryata kinsan yau akwai mkrnt.
    A zuciyarta tace ai ta isa shiryawa insha Allah tama shirya.
    Yana tun karar dakin nasu yaji kukan Shaheeda, da sauri ya karasa.
    zaune ya ganta tanata faman kuka itama Sapna tana gefe tana hawayen.
    DA sauri ya karasa wajanta tareda daukarta yana fadin lafiya yr kirki.
    Cikin kukan tace mama!
    Itama Sapna da sauri ta taso tana kukan tareda shigewa jikinsa tana fadin yaya dan Allah ka kaimu wajan mamanmu dan Allah yaya.
     Ya isa Sapna yanzu kuzo muje kuyi breakfast sai kitafi makaranta insha Allah nizanje na dauko ki daganan zan kaiki wajan Maman taki.
    Baba komai kinji muje.
Sannan ya fito dasu daga dakin.dakinsu Safiya ya shiga.
Umma na zaune kan kujera a falo.
    Zama yayi sannan ya gaidata bayabo ba fallasa ta amsa.
    Itama Sapna gaisheta tayi Amma bata amsa tataba.
     Kaji maryam bata da lafiya tana asibiti ko?
   Eh jiya ai inacan shiyasa ban shigo da dareba.
    Tasamu karuwa namiji Amma barai yazo.
    Fal taji farin ciki cikin zuciyarta Amma saita nuna bataji dadiba.
    Allah ya jikansa tafada duksuka amsa da ameen.
    Yabjinkin nata Itakuma.
    Toh dasauki za'a ace Amma harna taho bata farkaba.
    Allah sauwake de,ameen nan ma suka fada.
    Safiya dake zaune tana karyawa tunda suka shigo batayi maganaba ya juya ya tambayeta tareda fadin ke dama baki iya gaisuwaba.
      Ayyah kasan itama jiya da zazzabi ta kwana da nacema yau bazata makarantaba amma tunda exam suke nace taje.
    Hmmm! Murmushi Hafsat tayi dan tasan kawai Umma tayi hakanne dankar yaya yayi mata fadane.
    Allah ya sauwake yace.
Ammm Hafsat haduma yarannan breakfast pls.
    Toh tace nan ta shiga hada musu Umma kuwa sai hararar ta take itakuwa tayi kamar bata fantaba dama so take ta basu tana tsoran fada.
    Nan ta hado musu ta anje suka zauna su naci.kamaryasani yaji ltashi yatafi Har suka gama sannan yace toh kutaso na kaiku makarantar.


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fansclub💅🏻🌷


Written by Zeenaseer😘
[14/1 12:54] Zeeenaseeer: 🌳🌳       ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
              👑👑
                🌳
     MARAICHI❣
             NA
 Zainab Naseer Sarki
    (Zeenaseer😘)


0⃣7⃣

Makaranta ya kaisu sannan ya dawo da Shaheeda gida.
    Dakin shi ya nufa yayi wanka sannan ya shirya.
Gidan ya shigo rike da Shaheeda a hannunsa.
A cikin falo ya samu Umma da Hafsat suma sun shirya da alama asibitin zasu bisu.
   Yauwa Dan Asabe dama yanzu nake ce da Hafsat tazo taje ta gaya maka inzaka tafi muma muje mu dubata mana.
   Ahhh shikenan nan ma aina shirya saimu huce kawai.
Sannan suka fito suka tafi zawa asibitin.

Lokacin da suka isa tun a reception suka hadu da Naja gaisawa sukayi da ita.sannan ta amshi Shaheeda a hannun Hafsat.
   Ummace tace da ita yame jiki cikin nuna damuwar ta.
     Jiki da sauki de za'a ce.
   Toh Allah ya kara sauki Wallahi duk da ba shiri muke da yarinyar nan ba amma sai naji duk ba dadi.
    Allah Sarki  Naja tace,ina su safiya ko sun tafi makaranta?
   Wallahi sun tafi ita da Sapna da yake jarabawa ake nace su tafi makaranta insun dawo tunda yau ba islamiyya sai suzo.
    Gaskiya Allah ya bada sa'a.
    Dan Asabe ne yace ya jikin nata.
   Toh da sauki sunma canza mata daki yanzuma suna can za'a dau hoton kan agani.
   Toh Allah ya sauwake ni bara naje in en bauchin sunzo ayimin waya mun mayi waya da Maria tace itama insha Allah tana nan tahowa.
   Toh Allah ya kawo su lafiya.
   Ameen yace sannan ya kalli Umma yace nizan tafi zan aiko atafi da Ku in anjima.
   Toh saika dawo Allah bada sa'a abunda bata taba gayamai ba tunda suke.
   Ameen sgimade kawai ya fada sannan ya huce.
    Shaheeda kuwa tana jikin naja dayake ta Santa sosai kuma tana kaunarta sosai shiyasa koda dan Asabe zai tafi batayi kuka ba.
 
Bayan mintina 30 da tafiyar dan Asabe aka fito da ita.
Wannan karanma allurar bacci sukayi mata.
Likitan ne ya kirayi Naja zuwa office dinsa.
Nan tacema su Umma tana zuwa sannan ta mike dauke da Shaheeda a hannunta.
   Bayan ta shiga ta zauna ne.
   Sannan ya dubeta dakyau yace magana ta gaskiya bazamu cuce kuba komu ci muku kudi babu abunda muka gani cikin kwakwalwar tata saide in tatakin za'a Abi agurin haihu ta samu ciwon.dan Wallahi munyi binciken mu iya bin cike Amma babu abunda muka gani.
    Innalillahi wa'ina ilaihir raji'un taketa ambata bakinta ta toshe idanunta na hawaye tama kasa cewa komai.
    Hakuri zakiya hajiya addu'a zakuyita yimata kuma shawarar dazan baku shine Ku kaita gidan mahaukata kawai insha Allah zasuyi maganin matsallal tata.
    Kuka sosai Naja takeyi sabo da abunne ba'a cewa komai.
Itama Shaheeda dake hannun ta kukan ta fara.
Akafada ta sanyata tana hawaye tana lallashinta.
     Cikin muryar kuka tace shikenan liki insha Allah zamu kaita Amma ina jiran yn gidan mune su karaso daga bauchi sai asan yanda za'a yi.
    Ba damuwa insha Allah,Allah ya kawosu lafiya amma kirki sannan musu ki bari su karaso da Kansu.
     Toh! Sannan ta mike ta fito jikinta asan yaye toilet ta shiga sannan ta saba Shaheeda abayanta kukanta tasha dan batasan ta nunawa Umma akwai wata matsala.
Saida tagama ta wanke fuskarta sannan ta fito daga toilet din ta nufi gurin su ta zauna.
     Da Sauri Umma tace yamai jikin.
   Murmushi ta kakalo tare da fadin jiki da sauki.
    Yauwa dama haka akeso Allah ya kara sauki.
    Ameen Hafsat ta furta ita da Naja.


❣MARYAM❣
Mahaifin ta shararran dan kasuwane kuma dan boko ne.
   Matarsa guda daya yaransu hudu maza biyu mata biyu.
   Mahaifiyar su da suke kira hajiya macece mai mutunci,kauta dasan addini.
   Haka zalika mahaifin su.
   Yana dasan taimakon jama'a dakuma kauta shima.
    Babban dansa namijine yayi aure yana nan zaune agarin bauchi sunansa Yakubu suna kiransa da yaya.
   Sai na biyu shima namijine shima yayi aure harda yara shikuma Jamilu sai kuma Naja'atu dake aure anan kebbi sai kuma autarsu Maryam.
    Sun taso cikin gata da tarbiya wajan iyayansu,gashi suna Santa saboda itace auta haka zalika kowa agidan naji da ita kasancewar akwai dan nisa tsakaninta da Naja.
    Lokacin da naja tayi haihuwar ta biyune sunzo suna kebbi Ibrahim ya ganta.haka kuma ya kwanta mata.
    Kasancewar yace yan da mata Har biyu Babanta yace ta hakura dashi kawai amma ta nuna itade tana San sa.
    Haka akasha shagalin biki aka kawota nan kebbi.
   Naja taji ddi sosai saboda yar uwar tata ta dawo kusa da ita gashi unguwa daya tsakaninsu ba nisa.
 Hakan yayima Maryam ddi sosai kasan cewar gata ga yar uwata duk wani abunda ke damunta ita take gayama.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
Yana kwance kan gadonsa bayan sallah insha'i ta turo dakin nasa sanye da kayan bacci ajikinta.
    Zama tayi kusa dashi tare da fadin pls bby katashi inasan muyi magana dakai.
    Wata magana kuma salma pls ki zo mukwanta sai gobe mayi maganar ya fada yana matsowa kuwa da ita.
    Wani irin sai gobe kuma kasan abunda zan gayama kobme mahinmmancine.
   Pls bakida wata magana mai mahimmancin data huce mujinki.
    Hakama zakace kabari mana kaji abunda zan fada.
    Kan huyanta ya kwanto tareda fadin ina jinki.
    Amm dama zamuje bikine nida su mum Zariya 1wk zamuyi.
     Dagowa yayi yana kallanta tareda fadin wk kuma salma.
    Eh mana toh menene aciki bikin yn uwa nane ko kansu nakibzuwane.
    Gaskiya inde wk zakuyi bazakije.
   Haba Fahad wata irin magana kakeyine.
    Ko mawa yayi ya kwanta tareda juya mata baya.
   Maganafa nake maka Fahad ka juyamun baya.
    Nagama magana inkin yarda zakiyi 2 days ki dawo na barki Amma wk yayi yawa.
     Haba Fahad gaskiya baka yimin adalciba taya zakana hanani shiga cikin in uwana kai hanaka fita nakeyi.
    Enough pls salma abunda kike ya fara insana ni nake auranki ko ke kike aurena.
Nagama yanke hukunci in kinga dama kibi inkuma bakiga dama ba ga kofa nan u cn go.
    Mikewa tayi tareda fadin dama aiku maza haka kuke kafin Ku auri mutun kuna nunamai so da kauna Amma daya shigo gidanku sai kuna yimai yawo da hankali kuma Wallahi baka isa ka rabani da yn uwa naba.
     Alright haka kika fada naji bana sanki kuma bana kaunarki kuma na Riga na baki choice inknga dama ki dauka in kinga dama ki barshi.
Ke in fact babu inda zakije inkuma kika fita karki dawo min nan.
    Haka kafa shikenan u will c ta mike tare da janyo mai kofar da karfi ta fice.
    Kanshi ya dame dan kullum sai  salma ta samai headache amma ya kusa maganinta.
Ko mawa yayi ya kwanta.

Itama tana shiga daki kan gado tafada tana kuka meyasa Fahad ya ke mata irin wannan gaba daya ya canza mata kode wata yakeso.
     Wani kukan ta kuma fashewa dashi tabbas bazata iya rayuwa babu Fahad ba Amma meyasa baya kaunarta yanxu.
Da wannan tunanin tayi bacci.

    Koda gari ya waye kin hadamai breakfast tayi yanxu bata zuwa makaranta inda take teaching dan anyi Hutu.
    Yana fitowa da safe cikin shirinsa na office dama beyi tunanin zata hada maiba dan haka fita yayi batare da yaneme taba.
    Tana tsaye abakin window Har ya fita da motarsa tana kallansa.
Saida ya fice sannan ta dawo falon kitchen ta nufa ta hada abin karinta Amma gaba daya zuciyarta ta kasa nutsuwa dan tana mugun kwanar Fahad ba karya.
Wayarta ta dauko dan turamai sakon bada hakuri.
     Bayan tayi sallama sannan ta tura masa kamar haka:
 
        Know I've hurt u
     I didn't mean to.
I am sooooooooo sorry.
    Please forgive me🙏🏻

Sannan ta tura masa.
   Yana cikin driving yaji alert alamun an turo masa sako.ahankali ya dauko wayar ya duba ya gani shima murmushi yayi dan shima yana kaunar salma sosai.shima tura mata nasa yayi kamar haka.
 
       Baby ix OK.
  Nd am also sorry fr pls.you are d first and only person to touch my hrt wit passionate nd neverending Lov.
   I Lov u m wife❣

Tana cikin shan tea taji messages dinsa ya shigo dama shi take jira da sauri ta dauka ta bude.bayan ta karanta itama taji ddin hakan sosai dan haka tadau alkawarin cewa inde bai bartaba bazatajeba.
Wayar taketa faman kallo tana murmushi😊

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑

[11:08am]
Daidai wannan lokacin yn bauchi suka iso babban asibitin kebbi.
   Parking motarsu sukayi Hajiya da yaya ne suka zo sai kuma matar yayan Bilkisu.Dan Baban baya kasar yana Saudiya.
   Cikin asibitin suka shigo.
   Har lokacin Naja da Hafsat na nan zaune dan da dan Asabe ya turo mota su ummace kawai ta tafi ita Hafsat cewa tayi zata taho hakade ta hakura dande ganin mutane ta yarda Amma bata soba.
     Suna shigowa Naja ta hango su da sauri ta taso ta fada jikin Hajiyar tana kuka.
    Bilkisu ce itama da abun ya bata tausayi ta fara kwalla tana dafa bayan Najar.
    Yayan ne yace ya isa haka Naja'atu yanzu ina Maryam din take ya jikin nata.
     Itade Hafsat tana zaune rungume da Shaheeda tana kallansu itama kamar tayi kukan.
    Gaba daya suka dunguma dakin da Maryam din take Har Hafsat.
    Tun kafin su karasa suka fara jiyo ihu da sauri suka karasa banda naja dataja baya dan gaba daya kafafunta kasa daukarta sukayi nan ta zauna tareda zubawa dakin ido hawaye na zuba😢


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fansclub💅🏻🌷


Written by Zeenaseer😘
[14/1 12:54] Zeeenaseeer: 🌳🌳       ⚜        🌳🌳
🌳                              🌳
              👑👑
                 🌳
      MARAICHI❣
              NA
 Zainab Naseer Sarki
      (Zeenaseer😘)


0⃣9⃣

Rungume ta tayi tareda fadin zata dawo Amma saikin dena kuka kinji.
    Bazaki tashi ki karasa wanke wankenba kuma ki bar yarinyar nan karta kuma taba mana kwanika tayi mana kazanta.
    Zauna kinji Shaheeda yanzu zan karasa saina kaiki wajan Anty Naja amma kar kiyi kuka.
    Kanta ta gyada tareda gogema Sapna kwallar data fado mata kan fuskarta.
    Ahankali take tafiya dan duk jikinta yayi tsami harta karaso wajan.
    Saura kuma naji wannan magana a bakin wani saina kusan kashe ki dake da Shaheeda dukkan ku.
Kina jina ko?
    Da sauri ta gyada kanta tareda fadin eh.
   Sannan ta karasa wajan tanayi tana kwallah ga kayan da uban yawa Har ta gama tanayi tana jiyowa tana kallan Shaheeda dake zaune Har bacci ya dauketa ta kwanta agurin gashi Har rana ta taddo wajan.
    Ahankali ta mike dan kaita daki.
    Tana GAF da karasawa wajanta Safiya tace ina kuma zaki.
   Kamar zatayi kuka ta nuna Shaheeda tareda fadin tayi bacci kuma tana cikin rana shine zan kaita daki.ta karashe maganar tareda juyawa zata dauke ta.
    Huce kije saikin gama duka kin gyaramin wajan tukun zan ki dauketa Umma ta fada.
   Da kamar zatayi magana amma saita fasa tana juyawa tana kallanta harta koma tazauna taci gaba.
   Saida ta gama duka ta kwashe kwanikan ta share wajan sannan ta dawo ta dauki Shaheeda ta kaita daki ta kwantar da ita tareda tsora mata ido tana kallan fuskarta.
Ahankali ta shafa fuskarta tareda manna mata peck adan bakinta tana tunanin yanda mamansu take rayuwa dasu.
    Jin ana kiran sallah azhr ya sanyata mikewa alwala ta daura tayi sallah sannan ta rokama mamansu sauki gurin Allah itama baccin ne ya dauketa nan gurin.

       Hafsa na dawowa daga makaranta dakinsu ta nufa bayan tayima Umma sannu da gida sannan ta nufi toilet ta bama kanta shower sannan ta fito.saida tayi sallah taci abinci dan ita atunaninta su Sapna suna gidan Naja.
   Shiyasa bata ma name suba.
  Jakarta ta dauka sannan ta nufi dakin Umma de tana kallanta bat kula taba.
     Sapna ta gani kwance tana bacci ga Shaheeda bisa kujera bata ce musu komaiba.
    Daki ta nufa ta saka kaya sannan ta fito falan ta zauna.
     Shaheeda ce ta tashi tana ganin hafsa ta kama kuka.
    Lafiya Shaheeda menene kike kuka.
   Safiya da Umma ne suka doki ya Sapna.
    Toh ya kuri zansa dodo ya cinye su suma kinji amma fa karki gayama yaya dan Asabe dan in kika fada shima dodo cinyeshi zai yi .
    Kai ta gyada mata tareda fadin bazan fada ba.
    Yauwa yr kirki bara na dauko muku abinci nasan Baku ciba.sannan ta mike ta fita daga dakin.
    Bayan ta fitane Sapna ta mike ta nufi toilet ta zubama kanta shower dan duk jikinta radadi yake mata.sannan ta wanke bakinta ta fito.
     Lokacin Har hafsa ta fara bama Shaheeda abincin.
    Kallo daya tayima Sapna taga fuskarta da idanunta duk sun kumbura.
    Zama tayi tareda cewa ya hafsa sannun da dawowa.
     Janyo flask din abincin tayi tana zubawa.
    Me kika yima su Umma suka bigeki.
     Kallo daya tayima hafsa ta dukar da kanta kasa tana zuba abincin batareda da tace mata komai ba.
    Har ta gama zuba abincin sannan tace fada mukayi da Safiya. Daga nan bata kuma cewa komai ba ta fara cin abincin ta.
     Amma Sapna me yasa kike boyemin wani abun.
     Cikin muryar kuka idanunta na zubar da hawaye tace ya kibari kawai nace fada mukayi da safiya bakomai kuma.
      Dafata tayi tareda fadin kiyi hakuri kibar kuka ya isa haka.
Rungume hafsa tayi tareda cigaba da kuka.
    Ya isa haka Sapna kidena kukan nan haka.
    Dan Allah Ya hafsa ki rinka yima mama addu'a Allah yasa ta warke ta dawo wajan mu.
     Insha Allah ina yimatakuma zanci gaba dayi mata kinji maza kici abincinki kinsan in bakya cin abinci yaya fada zaiyi miki.
     Haka taci gaba da cin abincin badan tanajin dadin saba.
    Shaheeda kuwa cin abincin ta take tana kallan Sapna.
Suna hada ido Sapna ta sakar mata murmushi.

BAYAN WATA 4⚜
    Lokacin har anyi bikin Abba Ankawo Amarya Rahama.
    Rahma ko kadan bata da kunya batasan darajar kowaba kullum cikin fada suke da Abban kowa yanaji babu wanda ya isa yayi mata magana.
    Gashi kullum gidan cike yake da baki maza da mata.
  Haka zalika ta tsani dukkan wani mahaluki dake gidan.
     Haka shima dan Asabe yayi aure harma ya maida Shaheeda gurinsa kuma Alhmdullh ya sami mata ta gari kullum tana cikin samun kulawa.
   Dayake yanxu yayi nisa dasu ba kullum yake zuwaba yakanzo ya koma ne.
    Kuma yakan kawo Shaheeda taga Sapna kuma itama tana zuwa wajan ta.
  Ya kaisu bauchi Har sau uku Amma Har yanzu jikin mamansu ba sauki saide abunda yayi gaba.
   Kullum sapna abun tausayi agidan nan yanzu sun shiga  jss1.
   Kuma Har yanzu tana da ko karinta an sama Nana da hafsa rana dan suma Bilkisu za'ai nan da wata biyu.
Haka rayuwa ta kasance musu.
    Kullum in Umma na cikin kyara da tsangwamar sapna komai tayi ba daidaiva.
Wani zibin kuma ta sanya Abba yayi mata duka.
    Har ita matar Abban ta maida ta tamkar yr aiki.
  Dan sun hade kai da Umma
Allah Sarki Sapna ga hakuri gashi ko me za'a mata bata fada.hakanne ya ke sanya Hafsat jin haushinta tun tana magana Har ta gaji.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
Haka rayuwar gidan fahad yau suyi fada gobe su shirya dan yanzu salma tabar teaching kullum bata da Lokacin sa dab business takeyi.
    Ga shegen kishi amma bata iya kula da miji ba.kullum mummyn ciken fada takemai akan ya kara aure ko zai samu nutsuwa amma ko kadan yaki kamar wanda tamai asirivsaide suyita fada suna shiryawa.
   
Yauma tunda safe suka fara fadn da suka saba.
   Haba fahad kai kullum ka gwammace muyita fada kamar wasu yara gaskiya nina gaji.
    Shikenan nagaya miki banasan wannan business din naki saboda ko kadan bakya San kulawa dani.
    Toh so kake na goyaka na rinka yawo dakai kokuwa ya kakesan nayi maka.
Sai naga kamarma bakin ciki kake yiman Wallahi.
    Naji ina miki bakin ciki ni yawan da kikene bana kauna ki zauna mana agida arinka zuwa ana siyan kayan naki.
    Wallahi bazai yiyu ba kasan ina da kishi dan arinka Tara mata suna kalle min miji Allah ya kiyaye.
    Shikenan kije kiyi Wallahi aure zan kara.
   Wallahi Har abada bazaka yimin kishiyava mundin kuwa ta shigo gidan nan sunan ta gawa.
    Ko kulata beyiba ya fice daga gidan.
  Zama tayi kan kujera tareda fashewa da kuka.akan me fahad zai ambaci sunan data tsana duk duniya Wallahi  bazai sabova bara ya dawo gidan saiya gaya mata yar gidan ubanwa zai auro mata.


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fansclub 💅🏻🌷



Written by Zeenaseer😘
[14/1 12:54] Zeeenaseeer: 🌳🌳       ⚜        🌳🌳
🌳                              🌳
              👑👑
                 🌳
       MARAICHI❣
                NA
   Zainab Naseer Sarki
       (Zeenaseer😘)


1⃣1⃣

Ahankali ta karaso Har inda take.
   Jikintane ya kama rawa saboda tsabar tsoro.
   Saida tazo daidai da ita tareda yayi dan kwalin kanta ta kama shin shina huyan nata.
  Da sauri ta matsa daga kusa da ita tareda fadin dan Allah Anty Rahama kiyi hakuri.
    Murmushi tayi tare dafadin Sapna niba hani Abu zan miki ba jst inasan taimakon kine.
    Toh Anty ni yaya cewa yayi nayi kawai nayi miki shara dan Allah kiyi hakuri.
   Mtewww aikin banza ina nema miki hanyar da zakiji ddi Shikenan kin yima kanki.
Ta juya tareda shigewa daki.
   Tsugunnawa tayi tareda fashewa da kuka.wannan wani irin abunne kowa baya santa itade tashiga uku.
    Ahankali ta mike dan kar Abba ya kuma shigowa dan wani case dinne da ban.
Share falon tayi sannan ta nufi kitchen tayi wanke wanke ta gyara ko ina sannan ta dawo dakin shi bayan ta gama ne ta rasa yanda zatayi ta shiga dakin Rahma dan taga kamar bata da hankali.
Ahankali ta shiga bataga kowa acikin dakinba.karan ruwa taji kicin toilet hakan ya sa ta shiga dakin nan da nan ta gyara ko ina ta share.tana cikin mopping ta fito daga toilet din daure da wani dan karamin towel ko cinyarta be gama rufewa ba.
   Kanta akasa ta kara mopping inta dan itama bata mata magana ba.
  Bayan ta gama mopping ta zauna a folo tana jiranta ta fito dan ta gyara toilet din.
   Bata jimaba ta fito sanye da Riga top harmless da dan karamin wando bekai giwaba shima ta zubo da kitsan karinta kanana taci uwar make up a fuskarta.
    Tana gani ta fito tayi maza ta shige dakin toilet ta nufa tayi abunda zatayi ta gama sannan ta fito.
   Ahankali taje kusa da kafar Rahman tace Anty nagama nagama zan iya tafiya.
    Batare da tafara kallan taba tace Sapna kin fara period ne.
    Shiru ta tayi nadan Lokacin kafin tace Aa Anty.
  Murmushi tayi tare da fadin shikenan tashi ki tafi da yamma kizo inasan ganin ki.
   Toh nagode sai anjima ta fada tare da mikewa da sauri tabar dakin dan ita Rahman tsoro take bata.
Dama akwai mata yn iskanr.gaskiya abun mamaki ko kunyata bataji take yawo ahaka.
Tir! Allah ya kiyaye kwara da Allah yasa yr kirki bata nan da itama ta ganta ahaka.
    Da sauri tabar part din.
Koda ta shigo part dinsu ahankali tashiga dakinsu.
Toilet tanufa dan gyara jikinta yanda hafsa ta koya mata.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
Yaukam cikin haushi ta yini agidan dan gaba daya Kalmar aure da Fahad ya furta ta tayar mata da hankali.
     Yanda ya barta haka ya dawo ya tarda ta acikin gidan ko tsinke  bata kauda.
    Sallama yayi tareda maida kofar falon ya rufe.
Tana zaune kan kujera tana huci kamar wanda tayi dambe.tamaso bashi dariya amma ya daure fuska..
    Gabanshi ta mike ta tsaya tana kallansa kafin tace meyasa ko kadan Fahad bakasan zaman lafiya acikin gidan nan.kullum kai burinka bacin raina.
    Da mamaki yake kallanta tareda fadin amma sai yanzu nasan karatun da kikayi bashi da wani amfani.
   Ke Har kina tunanin matar da bata kula da mijinta za'a samu kwanciyar hankali acikin gidan.
    Kibani hanya ni ina da abinyi kinji na gaya miki.
Bangajeta yayi ya shige dakinsa.wanka yayi ya gyara jikinsa ya dauki key dinsa ya nufi gida dan cin abinci.
    Ina kuma kake tunanin zuwa.
   Saida yakai bakin kofa sannan ya ce da ita zance gurin budurwa ta sannan ya janyo gidan ya yi masa key.
   Ya shiga motar shi ya fice acikin gidan yana dariya.

Tana ganin ya rufe kofar ta nufo shi tana kiransa tareda buga kofar yayi banza da ita.
Tana ganin ya fita tayi maza ta nufi dakinta ko zataga wani makullin amma bata samuba.
    Dakin shi tanufa tana murdawa taji ya kulle dakin.
Wani irin koka  fashe dashi tabbas fahad na neman hallakata hira.
   Da gudu ta kuma nufo kofar falon ta a bugawa Amma babu mai jinta bare a bude mara.
    Hannunta ta Dora saman kanta tareda kwalla wani rin ihu ta durkushe anan wajan tana kuka.
    Dan ita Wallahi da ayi mata kishiya gwara a kasheta dan Wallahi bazata taba yandaba.
    Kuka sosai take famanyi tana tunanin yanzu tana can tana kalle mata mijinta.
Kamar mahaukaciya ta zauna ta tan kwashe kafafunta tana kuka wiwi wata na tare da mijinta tana jin muryar sa.


Shikuwa yana fita daga gidana,gidansu ya nufa yanata murmushi shi kadai cikin mota yasan duk inda hankalinta yake ya gama tashi.
   Allah Sarki salman sa  shima bazai taba yimata kishiyaba dan baiga matar dakai tasaba duk da bata cikamai dukkan hakkokin daya kamata mace ta gari tabaima mijinta amma yana jinta Har cikin zuciyarsa.
   Da wannan tunanin Har ya karaso gida.
Da sauri me gadi ya bude masa gate ya shiga da motarsa.
       Bayan yayi parking ne suka gaisa da ma'aikatan gidan.
Sannan ya shiga cikin gidan.
   A falo ya tanda dad da mom dinsa suna hira.
Da sallama ya shiga wajansu tareda gaidasu sannan ya zauna kan kujera.
   Dad dinsane ya kalle shi tare da fadin ya aiki.
   Alhmdullh ya fada yana shafa sajan fuskarsa.
   Madallah ya iyalin naka.
   Wallahi dad duk lafiya qlau.
   Masha Allah yanzu muke maganar kokarin aikinka dani da mom dinku.
    Wallahi kuwa dad ai muna kokari kam dan yanxuma insha Allah karshan watan nan zamu gama duk abunda ya kamata dan gane da saban company da za'a bude.
    Allah ya bada sa'a ya kuma taimaka dad ya fada.
    Ameen ya Allah mom ta amsa.
    Murmushi yayi tare da so sa kansa yana fadin Mom akwai abincin nan kuwa.
    Hararar shi tayi tare da fadin ban saniba.
Allah kude ku canza tsarin da kuka daukama kanku.tam nede na gaya ma.
    Gashican kaje ka diba.
   Dad ne yace nima ko abun yana damuna dan Har yanxu fahad bai isa da gidan Saba ko saiya kara mata tabiyune.
   Hmm! Shide ya sani waisu turawa aikuwa yinwa ba'a mata turanci ahhh tohh!
    Dariya yayi tare da fadin kwa nan nan zan kara aure mom saikin dinga cigiyata.
    Kaini huce kaban guri karyar banza.
   Dariya yayi sannan ya huce ya cika tumbinsa sannan ya dawo suka dan taba hira yace zai huce gida.
     Ai baka ci kai kadai ba kazo ka daukama madam din taka nasan itama tana da bukatar sa.
     Da kamar bazai sauka sai kuma yace toh kawo a kaimata sannan ya amsa ya yi musu sallama ya tafi.

.ita kuwa salma tana nan bakin kofa taci kuka harta koshi dan bakin ciki bacci ya dauketa.
    Karan bude dakinne ya tasheta da sauri ta mike tsaye.


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
 01 Amal fansclub 💅🏻🌷


Written by Zeenaseer😘
[14/1 12:54] Zeeenaseeer: 🌳🌳       ⚜        🌳🌳
🌳                             🌳
              👑👑
                🌳
     MARAICHI❣
            NA
  Zainab Naseer Sarki
    (Zeenaseer😘)


1⃣0⃣

Haka ta mike taci gaba da abunda take ranta duk ba ddi.

Shima yana fita gidansu ya nufa dan yasamu yayi breakfast dan ba sosai yakesan cin abinci restaurant yafisan na gida.
Dan yanzu kam Har mummyn shi ta gaji da magana akan matarsa.
Shima kuma bashi da burin kara auran,tunda yanzu ga guda dayar nan ta takura masa bashi da sakat akanta.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
   Tana kwance kan gadon su dan yau gaba daya tunda ta tashi batajin ddi cikinta keta faman ciwo.
Babu abunda tayi dan tana jin ko makaranta bazata iya zuwa ba.
    Hafsat da ta lura da hakan ta karaso kusa da ita tareda fadin Sapna lafiyarki qlau kuwa.
   Wallahi ya hafsa tun jiya da magriba nakejin jikina babu ddi ga ciki na sai faman jiwo yake.
   Amma kuma bakiyi maganaba aida na baki magani.
   Itade shiru tayi dan batajin ddin yin maganar ma.
    Toh ko kin fara period ne.
   Dayake tasani tunda ana koya musu a makaranta.
    Girgiza mata kai tayi tareda fadin aa.
   Nazata kema kin fara dan naga Safiya nayi.
   Yanzu kije kiyi wanka ki shirya tunda makaranta zaku tafi.
    Zandeyi wanka Amma ya Wallahi banjin zan iya zuwa makaranta.
   Toh tashi kije kiyi inyaso saiki karya kisha maganin ko kuwa.
    Mikewa tayi ta nufi toilet din tareda fadin toh.
    Tana shiga ta hada ruwan wankan.
   Tana cire kayan jikinta taji kamar pant dinta ya jiki.
Ga mamakinta tana dubawa taga jini ta dan tsorata duk da tasan komai game dashi amma gani take kamar yayi yawa.
    Leda ta dauka ta saka aciki sannan ta sa cikin dustbin.
   Saida tayi wankanta tsaf ta gama sannan ta fito daga toilet din gashi batasan yanda zata fadi maganar ba dan tana sana gayama ya hafsa ta bata patt.
   Yauwa kin gama hafsa tashigo dakin tana fada yauwa ga maganin nan da abinci inkin gama saiki sha kingani makaranta zan tafi safiya ta tafi.
    Toh! Ya hafsa dan Allah amm dan Allah nima ki bani dama yanzu da zanyi wanka na ga jinin yazo.
    Murmushi tayi tareda fadin kice in matan mama an girma tana dariya ta nufi wardrobe ta dauko mata always sabowa ko budeta ba'a yiba.
Sannan ta ce mata gashinan kinsan yanda ake sawa kona koya miki.
    Kanta akasa dan kunya takeji take na iya.
   Yawwa yr kirki gashinan to kisaka da kinji ta jike ta fara damun ki,saiki canza kisaka wata ita kuma ki saka cikin leda ki kai dustbin din waje karki anje cikin toilet.
    Toh nagode yaya saikin dawo.
    Tam! Natafi tafada tare da fita daga dakin.
    Murmushi tayi tareda janyowa ta duba ta sosai sannan ta sanya ta saka kayanta ta gyara gashinta dan tayi tsifa ba'a mata kitso ba.
    Tana cikin karyawa taji Umma na kwala mata kira dan taga bata je makaranta ba.
   Da sauri ta anje abincin ko magani bata shaba ta mike ta nufi dakin nata.
    Tana shiga Abba tagani zaune kan kujera gabanta ne yayi mugun faduwa dan duk duniya babu wanda ta tsana kamar sa.
    Zaune yake kan kujera yana dan wayar shi yaci magani ko murmushi baya yi suna hira da Umman tashi jefi jefi.
    Asanyaye ta shigo dakin tareda durkusa ya ina kwana!
    Ko kallan idan take beyiba bare ya amsa mata sallamar ta.
    Sannan ta jiyo ta gaida Umman.
    Lafy kawai tace da ita bata kuma mata magana ba Har ta fara gajiya da tsugunnan da take sai can yace.
     Kinsan bakije makaranta me ya habaki zuwa kiyima Bilkisu abunda zakiyi mata.
     A zuciyar tace lallai ku din nan inba doleba me zai hanani zuwa makarantar dama na sani nayi tafi yata maybe danafi samun kulawa.
    Ba magana ake ba magana ake mikiba kina jin mutane kinyi shiru.
    Firjita tayi tareda fadin Umma Wallahi bani da lafiyane shiy...
   Tsawa ya daka mata wata ta sanyata mikewa zata gudu.
  Dawo nan ki tsaya ya nuna mata gurin da zata tsaya kusa da shi.
   Gaba daya jikinta rawa yake gaba daya ta nemi Ciwan ta rasa.
  Ubanme yake damun ki?
    Batasan Lokacin da tace babu komai.
   Wato mu sa'anin was an kine ko?
   Hawaye ta fara ta hada hannayanta tareda fadin dan Allah yaya kayi hakuri Wallahi ba karya nakeba.
   Naji huce waje kiyi frog jump kuma banasan ki dena saina fito.
    Da sauri ta durkusa tareda rike kafafuwansa tana kuka dan Allah yaya kayi hakuri Wallahi cikina ke ciwo kuma idan nayi muguwa zanyi.
   Banza yayi da ita tanata faman kuka agabanshi.
   Ita kuwa Umman tashi tayi ta shige dakinta ko ajikinta.
    Tashito kibar gurin nan kuma kafin na shigo kin gama mata komai.
    Jikinta Har barri yake tace toh.da sauri ta mike kai tsaya part dinsa ta nufa Dan kota maganinta batayi ta nufi dakin.
    Koda ta shiga falon kamar anyi party yayi kace kace gaba daya ko ina an lala tashi.
    Batasan ta inda zata fara aikinba.
    Tana nan tsaye Rahama ta fito daga ita sai pant da bra ajikinta.
Ta zuna kan kujera tana kallan Sapna.
    Da sauri ta rufe idanunta da hannunta kirjinta na bugawa.
    Cikin wata muryar tace meya haka Sapna zoki zauna inasan magana dake.
    Kasa ko motsi tayi daga inda take.
    Shikenan tunda bazaki zoba ni bara naxo...


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fansclub 💅🏻🌷


Written by Zeenaseer😘
[14/1 12:54] Zeeenaseeer: 🌳🌳       ⚜        🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                 🌳
      MARAICHI❣
             NA
  Zainab Naseer Sarki
     ( Zeenaseer😘)


1⃣2⃣

Daga ina kuma kake? tambayar da tayimai kenan.
Shigewa yayi cikin dakin da flask din dake hannunsa.
   Da sauri tabi bayansa tareda shan gabansa.
Fahad magana fa nakeyima.
   Tsayawa yayi cak yana kallanta.
   Toh ina jinki fadi!
 Daga ina kake? Na tambayaeka.
   Flask din hannunsa ya mika mata tareda fadin daga gurin wanda ta Fiki sona da kaunata kum burinta koda yaushe ta ganni cikin farinci.
    Wani ihu ta kallah tareda sakin flask din hannunta tayi kuka kura ta shako huyan rigarsa.
    Ni zaka yima haka Fahad, amanata kakesan ci Wallahi baka isaba ta fada tareda fashewa da kuka.
   Dariya ya kama tareda fadin ya isa haka,salma nema kike ki zautani bakya jin maganata ko kadan kamar ba nine mijinkiba sannan in nace zan karo mata kiranka Abu kamar mahaukaciya.
    Zaunar da ita yayi kan kujera sannan shima ya zauna tareda fadin.
    Look in kinasan muyi zaman mu mubiyu cikin gidan nan tofa dule sai kina kula dani.
   Cikin muryar kuka tace amma fahad meye bana yima.
    Aww! Hakama za kice ai basu da adadi sallama.
    Sai kinga dama zaki yimin girki,gyaran dakinama saikinga dama haka shima gidan kuma ance a kayo yar aiki kince aa.bama wannan ba yaushe raban da kibani hakin aurena dake kanki.bakyajin maganata ahakan kike tunanin kina kula dani.
    Shiru tayi tana wasa da yatsun hannunta saboda tasan abunda yake fada hakanne amma taya zata iya duk abubuwan nan bayan ita ba jaka bace.
    Amma fahad ya kakesan nayi da aikin gidan nan.
    So kinga dauko yr aiki wajibine tunda bazai yiyu muna zama cikin sharaba kamar mahaukata ko dabbobima sun San su zauna aguri mekyau balle mu mutane.yakamata ki canja shawara.
    Kuma ni daga wajan mom nake Har tafada abinci in kawo miki gashi kuma kin xubar.
Peck ya manna mata a kumato tareda fadin nyt.
   Ya mike ya nufi dakinsa yana tunanin irin haukan salma.
   Itama batareda ta dauke flask din da abincin ta barsu anan tayi tafiyarta dakinta.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
  Bayan ta gama gyara jikinta tadan shingida ta huta dan ta gaji sosai ga cikinta da Har yanzu yana dan murdawa kadan kadan.
     Sallamar hafsace ta sanyata mike zaune.
  Zama tayi kan kujera tare da fadin wash Allah na.
    Ya hafsa sannu da dawowa amma naga yau kin dawo da huri.
   Wallahi kam kinsan na tafi da huri tunda exam muke shiyasa na dawo ya cikin naki?
    Da sauki mah..
  Amma bakiyi wani aikibako.
   Eh ta gyada mata kai tana kallan kafarta.
  Murmushi tari maras sauti dan rasan Sapna batasan gaya mata gaskiya shiyasa ta boye mata amma tasan sun sata aiki.
  Toh bara na dan watsa ruwa nayi sallah naci abinci danna gaji.
    Tana shiga daki ta koma ta kwanta da tafisan jinta akwance.nan tunanin Shaheeda ya fado mata sun jima basu haduba murmushi tayi kwallah na zubo mata ta gefan idanunta ko ba komai tanajin dadi Shaheeda na rayuwa me kyau dan Anty Zee na kula da ita (matar dan Asabe).


Baccine me nauyi ya dauketa ba ita ta farka ba sai bayan la'asr.
   Hafsa na sane taki tashinta dan ta barta ta hutane sosai.
    Tana farkawa toilet ta nufa dan gyara jikinta.bayan ta fitone taga hafsa azaune.
   Juyowa tayi tare da fadin Sapna harkin tashi aikinsha bacci.
    Murmushi tayi Wallahi nima nayi mamakina Har nakai wannan lokacin ina bacci.
    Hmmm Sapna kenan akwai gajiya a jikinki amma sai kina musa min kije ga abincinki can kici na kuma kara dauko miki maganin.
     Toh ya hafsa na gode ta fita daga dakin dan ita kanta tausayin kanta takeji yanda ta yi rashin uwa wanda hakan yasa ta zama marainiya.
     Abincinki ta dauko tasa agaba amma gaba daya batamin zata iya ko loma daya.
Kallan shi kawai take tana yamutsashi da lokaci.
Ahankali ta matsa ta jingina da kujera tana kallan fankar dakin yanda take juyawa.
    Nan ta rinka tuna abubuwa ita da Maman ta da yr kanwarta..
    Tana shigowa dakin ta ganta azaune ta sanya kafa ta buge ta.
   Da sauri ta firgita ta mike tare da fadin haba safiya meye haka zaki tureni kamar wata dabba.
    Tohke kina tunanin mutunce kamar kowa ai baki da maraba da dabbobi.
Kinaji ana faman kwala miki kira amma sabo da tsabar akuyanci kikayi shiru kinajin mutane.
    Toh kije Anty Rahma ke kiranki.
    Kice baza tazoba mutumma bashi da lafiya amma sai an takura shi.in wani abun za'a mata ba gakiba.
    Oohoo! Dai nide ita tace na kirata inkuma taki zuwa tasan sauran.
     Eh kije ki gaya mata nina fadi hakan hafsa ta kara bada ban maras kunya.
    Gaskiya ni kidaina cemin maras kunya bazai yiyu daga an aikoni ki ranka gayamin maganaba.
    Tasowa tayi Har kusa da ita tana tsaye itama.
   Na gaya miki sai kidau mtaki.
  Itade Sapna tana tsaye dan batasan abunda zaizo ya biyo baya ayi mata duka ba lafiya ba.
    Ya hafsa dan Allah kiyi hakuri bara naje.
     Wallahi bazaki ba Sapna tasa safiya tayi mata koma menene aiba lafiya garekiba koma dukanne saide ni a dakeni ko kuma mu biyun.
    Mtewww aikin banza ku kuka sani.
   Tassss ta dauketa da mari tare da hankdata tsakar gida sannan tace Wallahi kika yimin wani iskanci yan zan karyaki inga ubanda ya tsaya miki.
   Cikin murar kuka tace ubankine ya tsaya min shigeya tsinan niya..
  Aikuwa fitowa tayi daga dakin tashiga ball da ita tana ihu.
     Da gudu Umma ta fito tare da bangaje hafsa daga jikin Safiya.
    Amma kide Wallahi hafsa baki da mutunci yanzu akan wannan tsinannan yarinya kike dukan kanwarki ciki daya.
    Ai itama kanwa tace wandama ta fiyemin safiya da ita so dubu Wallahi.
   Lallai hafsa kin rainani harkin gayamin.
  Sallamar Abba ce ta katseta da maganar da takeyi.
   Yawwa dan halak dan Allah zoka targadamun wannan yarinyar.
    Kallan hafsa yayi dan basa shiri ko kadan yace da ita.
Ke meta miki kika daketa.
   Zagina tayi Nikum nadau mataki tunda itadin kanwa tace.
    Kallo sa ya maida kan Safiya dake kuka jikin Umma yace meyasa kika zageta.
    Wallahi yaya ba zaginta nayiba daga nacewa Sapna Anty Rahma na kiranta shine ya hafsa tace bazata inje ince bata da lafiya.
     Ke akan wannan ne kikayi mata wannan dukan..
    Itade Sapna na gefe arakube kamar munafuka jikinta sai rawa yake saboda tsoro.
    Amma ai itama tamin rashin kunya.
    Baxakimin shiruba saina ballaki dan uwarki.
    Kallan Sapna yayi dahar Lokacin jikinta rawa yake yace huce kije kiran da take miki.
   Rike ta tayi tare da fadin Wallahi fa bata da lafiya.
     Ina wasa dake bazaki saketanba ko mutuwa take ba rashin lafiya ba.
    Toh in abun na tsakani da Allah ne atura Safiya mana ko ita din yar aikice.
   Da gudu yayo kanta ya kama dukanta.
Tana ihu tana kuka tana rikeda Sapna Wallahi yau yaya ko kasheni zakayi bazataba wannan ai zalincine.
    Kamar Dada tunzurashi take duka biyun ya hada yana kwallo dasu...


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fansclub 💅🏻🌷


Written by Zeenaseer😘
[14/1 12:54] Zeeenaseeer: 🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                 🌳
       MARAICHI❣
                NA
  Zainab Naseer Sarki
     ( Zeenaseer😘)


1⃣3⃣


Sai da Umma tamasa magana sannan ya rabu dasu amma gaba dayansu sunji jiki da ko motsin kirki da kyar sukeyi.
   Gwara ita Sapna ta saba amma hafsa raban da a daketa harta mantah.

Sai faman huci yake ya kuma dakawa sapna tsawa baza ki tashiba saina miki wanda ya fi wannan.
   Gaba daya bata iya kukan hawayene wani kebin wani gaba daya jikinta babu inda baya mata ciwo.
Jikinta na karkawa Har dingisawa take haka ta lallaba ta nufi part dinsa kamar ta mutu ta huta takeji.
     Kafin ta karasa dakin ta tsaya ta fashe da wani irin kuka gaba daya batajin ddin rayuwata abun ya isheta tun kafin ta zama babba gaba daya sun lalata mata rayuwa konina taban dukane ajikinta.
   
Ba kowa tsakar gidan sai hafsa.
Da ker ta lallaba ta shige daki saboda kafarta data rike.
   Toilet ta nufa ta hada ruwan zafi dan tabbas saita gasa jikinta gaba daya tausayin Sapna take ji haka ta daure ta gasa jikinta.
Riga maras nauyi ta sanya sannan tasha magani ta kunna fanka ta kwanta nan da nan zazzabi ya rufeta tabbas Sapna taci gaba da rayuwar gidan nan wata rana sai ta mutu.


     Saida tasha kukanta ta koshi sannan ta fude kofar dakin Har muryar ta ta dashe sabo da kuka.
   Tana zaune kan kujera taci wasu en iskan kaya ba alamun murmushi a fuskarta.
    Ahankali ta karaso kusa da ita tareda durkusawa Har lokacin hawayen na zubowa daga idanunta.
    Dan girma Allah Anty kiyi hakuri yaya yama dakeni dan Allah ta kuma fashewa da kuka.
    Ko kallanta batayi saida tayi kukanta mai isarta sannan tayi shiru.
   Kin gama kukan ?
  Eh ta gyada mata kai to tashi kije cikin wardrobe dina na manta ban baki inner wears dina ki wankemin dazu kuma sun taru da yawa.
    Toh tamike ta nufi dakin da sauri.
   Har takusa kaiwa bakin kofa tace keh dakata.
Saura kimin jika jika Wallahi in basu fitaba saikin sake wankewa ko zaki kwana kinayi bai dameniba.
    Toh insha Allah, jikinta sai bari yake dan batasan yin ko kuskure
Daya akuma dukanta dan tana da tambacin ana kuma dukanta mutuwama zatayi.
     Tana shiga ta daukosu masu uban yawa sai faman tsami suke.
 Haka ta hada ta shiga baya inda suke dibar ruwa ta shiga wankewa iya,iyawarta Har aka kira sallah magrib bata gamaba sai gaf da insha ta gama sannan ta shigo falon da shiga inda zata shanya mata.
    Batama lura dasuba ta kusa kaiwa corridor da zata shiga ta kira sunan ta.
    Da sauri ta juyo dan tama tsorata.
Naam.
   Tana kwance jikin Abba sai kace mage shikuma sai wani kallan TV yake kamar ta kashe su da haushi.
    Zo muga irin wanki da kikamin karki ahanyamin kaya basu fitaba.
    Nan danan jikinta yayi sanyi dan tasan ba mutunci gareta baza iya cewa basu fitaba.
Amma tas suka fita duk taji ciwo a hannunta saboda dirza su da takeyi.
    Gashi ta mika mata bokitin tana karkawa.
   Tassss! Baki da hankaline haka aka koya miki wanki agidanku.
    Cilla mata bokin tayi Har kanta ya buga nan da nan gurin ta tashi.
 Haba Dallah kalli kayan duk basubfitaba take fadawa Abba.
    Shikuma yace da ita toh ai saiki tashi ki kuma wanke mata.
    Kwallah fal idanta ta mike ta dauki bokitin ta koma dashi.

    Tana kuka tana wankin ga hannunta sai jini yake kanta ma yana ta ciwo kai ko inama ciwo yake mata gaba daya tama rasa abunda zatayi dan kukanma ta gaji da yinsa.
     Sai 10pm ta gama wankin sannan ta dauka ta tafi dan ta nuna mata amma basa falon.
  Tafiya tayi ta shanya mata kayan sannan ta fita zuwa daki.
    Tana shiga bataga hafsa a falonba zama tayi kan kujera tana hutawa.
     Idanunta ta lumshe hawayen na zuba ta gefan idanunta.
    Ahankali ta fito daga dakin ganin Sapna zaune kan kujera ta karaso kusa da ita ta zauna tareda dafata.
   Idanunta ta bude ahankali kwallar data makale takarsa zubowa.
    Itama hafsa kwallar take ahankali ta sanya hanunta tana sharemata kwallar tareda girgiza mata kai alamun ta dena kuka.
    Cikin muryar kuka tace dan Allah ya hafsa kiyi hakuri duk ni naja miki wall......
  Rufe mata baki tayi da hannunta tareda rungume.
   Ba laifinki bane Sapna nice naja miki duka dan Allah kiyi hakuri tana jikin hafsar tana ta faman kuka.
    Ya hafsa wai meyasa kowa baya sona ko inayin Abu marar kyaune Wallahi zan dena dan Allah me nakeyi.
    Shhhhh! Babu wanda ya tsaneki ki bar wannan maganar.kowa yana sanki kuma kece meyin Abu mekyau babu abunda kike mara kyau.
Kandarece Allah ya dora miki tun kina yarinyarki.ki rinka addu'a Allah ubangiji ya sa kicinye jarabawar nan kinji.
   Gyada kanta tayi tare da fadin insha Allah.
       Yawwa yr Albarka kuma ko baki da lafy kina daurewa kina zuwa makaranta kinji.
Maza kije kiyi sallah kizo kici abinci.
    Ahankali ta raba jikinta dana hafsa ta mike ta nufi toilet.
    Ahankali hafsa ta sauke Ajjiyar zuciya ta jingina da  jikin kujerar tana tunanin yanda rayuwar Sapna zata kasance nan gaba.

     Saida ta yi wanka tayi sallah sannan taci abinci hafsa ta bata maganin tasha.
     Kwanciya sukayi kan gado.
   Bara nayi miki massage princess kai ya hafsa nice princess din.
     Sosaima kuwa kinma fi princess agurina.
     Ahankali ta rinka danna mata kafarta da jikinta.
    Itama taji ddi sosai saida ta tuna da mamansu lokacin da suke mata ita da Shaheeda suna dariya.
    Hawaye ne ya gangaro mata a haka Har bcci ya dauketa.. 
      Saida hafsa taga tayi bacci sannan ta matsa kusa da fuskarta tana da dakallanta.
     Ta kara fari duk ta fada fuskar tayi fayau dama ba Makeup take ba.
      Addu'a tayi musu sannan ta safe jikinsu da ita...☺


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
   01 Amal fansclub  💅🏻🌷


Written by Zeenaseer😘
[14/1 12:54] Zeeenaseeer: 🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
              👑👑
                🌳
      MARAICHI❣
           NA
  Zainab Naseer Sarki
      (Zeenaseer😘)


1⃣4⃣


🌺🌺
    I dedicated dis  page to u Anty Rabi'at,Ur d most special person in my life.ur my philosopher,guide nd lot more.wishing u all d season's happiness dis heartfelt can bring!.
  Lov u more nd more Anty Rabi'at.
                             🌺🌺


⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
........{7:30am}.........
     Fahad ne ya fito sanya cikin suit ash da red tie.yayi kyau sosai.
   Baiga kowa cikin falonba yasan bata tashiba kansa kawai ya girgiza dan baimasan yanda zaiyi da itaba.
    Nan inda flask din jiya ta yarda shi nan ya tanda shi,shikuwa sauri yake famanyi dan bazai iya bata lokacin saba.
    Fita yayi tare da kullo kofar falon da sauri yake yi.
 

   Bai jima da fitaba itama ta fito tasan ko ba'a fadaba ya fita.
Zama tayi kan kujera tana kallan yanda falon yiyi mugun dirty amma ita bazata iya gyara shiba dan gani take aikin yafi karfinta.
    Mikewa tayi ta nufi kitchen ta Dora abunda zatayi breakfast.
   Bayan ta gama karyawa ne ta shiga toilet ta tsan tsar kwalliyar ta.sannan ta dau key din motarta dan tana da gurin zuwa.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
   Bayan sun idar da sallah komawa sukayi suka kwanta dan yau hafsa bazata makaranta ba.
    Sapna kuwa wanka ta shiga nan danan tayi kayanta ta gama ta fito ta shirya cikin uniform din ckul dinsu.
   Hafsat ce ta dauko mata breakfast dinta sannan ta sanyata agaba da saita cinye dan taga kwana biyu batasan cin abinci gashi duk ta rame..
    Tana ci suna dan taba hira Har ta koshi sannan hafsa ta dauko kudin makarantar ta tabata dan dama Dan Asabe ke nawa kowa nashi sai tabama hafsa ta ajje mata.
  Sallama ta mata sannan ta fito ta nufi waje dan dama tun tuni Umma ta hanata gaisar da ita.
    Cikin mota ta shiga daga gidan gaba dan Safiya ke zama baya.
Kai tsaye makaranta aka nufa dasu tunda suka tafi babu wanda yake magana cikin motar sai karan radio da take tayi.
     A haka Har suka isa.
Bayan sun nufi class dinsu da yake class daya suke.desk dinsu ta nufa ita da kawarta Husnah.
    Bayan ta zaunane Hausa ke tmbyrta ya jikin nata.
    Da sauki tace da ita.
   Wai nema ke damun ki.
   Hmmm! Kawai dan Ciwan cikine.
   Allah ya sauwake ko de kema abunne yazu ta fada cike da zolaya.
   Kede kika sani koma me nene.
    Hahahhaa nasani ko kawar tawa ta girma.
    Toh bashi bane kawaide banajin ddine.
  Murmushi tayi tareda fadin jiya an bada Assignment ne.
  Aa Wallahi ba malamin daya bada..
  Yawwa Har naji ddi.


  Nan suka fara darasi Har zuwa lokacin da aka tashi tara.
     Suna zaune cikin class ita da Husnah da yake Sapna batasan hayaniya shiyasa bata fita tara.sunata hira suna dariya abunsu.
    Wata kawar safiyace ta mike tare da fadin hmmm ai duk wanda kaga baya fita break toh munafikine ko barawo.
   Ita de Sapna tasan dasu ake amma taki kulawa,Har Husnah zatayi magana tayi mata nuni da tabari dan Allah.
    Ywwa kuma Wallahi safiya muka nemi abunmu muka rasa Wallahi sai an biya mu.
    Husnah data kasa hakuri tace idanda ubanda ya isa ya hana sai mu gani.
Waya sanima ko kune barayin.
    Safiya ce tace ke Husnah badake mukeba saboda haka babu abunda ya dameki..
    Damu kuke mana su waya cikin ajin ko angaya muku munajin tsoran kune.
    Tasowa suka yi aikuwa itama ta tsalako ta nufe su alamun za'a ayi fada kenan.
    Sapna dake rubuta ta mike tare da fadin dan Allah kuyi hakuri munji mune amma kr kuyi fada pls.
     Banzaye marassa karfi safiya ta fada.
    Sapna ki rabu dani na koyawa yara hankali.
    Littafin ta ta dauka tare da fadin nina bar muku class din.
    Nan kuwa suka matso dama Husnah karfi gareta nan akahau fada harta basama Safiya baki.
    Nan aka kai kara gurin Auntynsu ta dau mataki sannan ta yima Safiya duka dan itada kawarta ne masu tsokana.

     Duk da safiya bataji dadin abunda ya faruba.gaba daya tunanin ta yana gida krtayi mata sharri a bugeta.
      Koda aka tashi da me daukar su yazo haka suka shiga gaba daya jikin Sapna yayi sanyi dan tsoro ji take kamar a yardata kan hanya.
     Da wannan tunanin Har suka iso gida.
   Da sauri Safiya ta shige gida tana kuka.
  Gaba daya hankalin Sapna ya tashi dan gaba dayama da ker take iya daga kafarta harta shigo gidan kasa hucewa tayi ta tsaya bakin rijiya tana rabe rabe.

     Tana shiga ta yarda Jakarta ta fada kan Umma tana kuka.
   Lafiya yar lele waya tafaki.
   Da gudu tayo waje tana fadin saina kasheta dan uwarta tunda tasa aka bugeni.
     Da sauri Umma ta biyota tana kiranta.
    Itama hafsa dake zaune a falo taji kamar karan kuka ya sanyata fitowa.

      Tana tsaye bakin rijiya ta anje jikarta kusa da kafa funta tana hawaye tana kallan kasa.
     Tana kara sowa da gudu ta turata baya.
Nan santsi ya kwasheta kanta ya bugu gaba daya ta fada cikin rijiyar.
    Wani irin ihu hafsa ta buga tareda yowa wajan da gudu.


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fansclub 💅🏻🌷


Written by Zeenaseer😘
[14/1 12:54] Zeeenaseeer: 🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                 🌳
       MARAICHI❣
                NA
  Zainab Naseer Sarki
     ( Zeenaseer😘)


1⃣3⃣


Sai da Umma tamasa magana sannan ya rabu dasu amma gaba dayansu sunji jiki da ko motsin kirki da kyar sukeyi.
   Gwara ita Sapna ta saba amma hafsa raban da a daketa harta mantah.

Sai faman huci yake ya kuma dakawa sapna tsawa baza ki tashiba saina miki wanda ya fi wannan.
   Gaba daya bata iya kukan hawayene wani kebin wani gaba daya jikinta babu inda baya mata ciwo.
Jikinta na karkawa Har dingisawa take haka ta lallaba ta nufi part dinsa kamar ta mutu ta huta takeji.
     Kafin ta karasa dakin ta tsaya ta fashe da wani irin kuka gaba daya batajin ddin rayuwata abun ya isheta tun kafin ta zama babba gaba daya sun lalata mata rayuwa konina taban dukane ajikinta.
   
Ba kowa tsakar gidan sai hafsa.
Da ker ta lallaba ta shige daki saboda kafarta data rike.
   Toilet ta nufa ta hada ruwan zafi dan tabbas saita gasa jikinta gaba daya tausayin Sapna take ji haka ta daure ta gasa jikinta.
Riga maras nauyi ta sanya sannan tasha magani ta kunna fanka ta kwanta nan da nan zazzabi ya rufeta tabbas Sapna taci gaba da rayuwar gidan nan wata rana sai ta mutu.


     Saida tasha kukanta ta koshi sannan ta fude kofar dakin Har muryar ta ta dashe sabo da kuka.
   Tana zaune kan kujera taci wasu en iskan kaya ba alamun murmushi a fuskarta.
    Ahankali ta karaso kusa da ita tareda durkusawa Har lokacin hawayen na zubowa daga idanunta.
    Dan girma Allah Anty kiyi hakuri yaya yama dakeni dan Allah ta kuma fashewa da kuka.
    Ko kallanta batayi saida tayi kukanta mai isarta sannan tayi shiru.
   Kin gama kukan ?
  Eh ta gyada mata kai to tashi kije cikin wardrobe dina na manta ban baki inner wears dina ki wankemin dazu kuma sun taru da yawa.
    Toh tamike ta nufi dakin da sauri.
   Har takusa kaiwa bakin kofa tace keh dakata.
Saura kimin jika jika Wallahi in basu fitaba saikin sake wankewa ko zaki kwana kinayi bai dameniba.
    Toh insha Allah, jikinta sai bari yake dan batasan yin ko kuskure
Daya akuma dukanta dan tana da tambacin ana kuma dukanta mutuwama zatayi.
     Tana shiga ta daukosu masu uban yawa sai faman tsami suke.
 Haka ta hada ta shiga baya inda suke dibar ruwa ta shiga wankewa iya,iyawarta Har aka kira sallah magrib bata gamaba sai gaf da insha ta gama sannan ta shigo falon da shiga inda zata shanya mata.
    Batama lura dasuba ta kusa kaiwa corridor da zata shiga ta kira sunan ta.
    Da sauri ta juyo dan tama tsorata.
Naam.
   Tana kwance jikin Abba sai kace mage shikuma sai wani kallan TV yake kamar ta kashe su da haushi.
    Zo muga irin wanki da kikamin karki ahanyamin kaya basu fitaba.
    Nan danan jikinta yayi sanyi dan tasan ba mutunci gareta baza iya cewa basu fitaba.
Amma tas suka fita duk taji ciwo a hannunta saboda dirza su da takeyi.
    Gashi ta mika mata bokitin tana karkawa.
   Tassss! Baki da hankaline haka aka koya miki wanki agidanku.
    Cilla mata bokin tayi Har kanta ya buga nan da nan gurin ta tashi.
 Haba Dallah kalli kayan duk basubfitaba take fadawa Abba.
    Shikuma yace da ita toh ai saiki tashi ki kuma wanke mata.
    Kwallah fal idanta ta mike ta dauki bokitin ta koma dashi.

    Tana kuka tana wankin ga hannunta sai jini yake kanta ma yana ta ciwo kai ko inama ciwo yake mata gaba daya tama rasa abunda zatayi dan kukanma ta gaji da yinsa.
     Sai 10pm ta gama wankin sannan ta dauka ta tafi dan ta nuna mata amma basa falon.
  Tafiya tayi ta shanya mata kayan sannan ta fita zuwa daki.
    Tana shiga bataga hafsa a falonba zama tayi kan kujera tana hutawa.
     Idanunta ta lumshe hawayen na zuba ta gefan idanunta.
    Ahankali ta fito daga dakin ganin Sapna zaune kan kujera ta karaso kusa da ita ta zauna tareda dafata.
   Idanunta ta bude ahankali kwallar data makale takarsa zubowa.
    Itama hafsa kwallar take ahankali ta sanya hanunta tana sharemata kwallar tareda girgiza mata kai alamun ta dena kuka.
    Cikin muryar kuka tace dan Allah ya hafsa kiyi hakuri duk ni naja miki wall......
  Rufe mata baki tayi da hannunta tareda rungume.
   Ba laifinki bane Sapna nice naja miki duka dan Allah kiyi hakuri tana jikin hafsar tana ta faman kuka.
    Ya hafsa wai meyasa kowa baya sona ko inayin Abu marar kyaune Wallahi zan dena dan Allah me nakeyi.
    Shhhhh! Babu wanda ya tsaneki ki bar wannan maganar.kowa yana sanki kuma kece meyin Abu mekyau babu abunda kike mara kyau.
Kandarece Allah ya dora miki tun kina yarinyarki.ki rinka addu'a Allah ubangiji ya sa kicinye jarabawar nan kinji.
   Gyada kanta tayi tare da fadin insha Allah.
       Yawwa yr Albarka kuma ko baki da lafy kina daurewa kina zuwa makaranta kinji.
Maza kije kiyi sallah kizo kici abinci.
    Ahankali ta raba jikinta dana hafsa ta mike ta nufi toilet.
    Ahankali hafsa ta sauke Ajjiyar zuciya ta jingina da  jikin kujerar tana tunanin yanda rayuwar Sapna zata kasance nan gaba.

     Saida ta yi wanka tayi sallah sannan taci abinci hafsa ta bata maganin tasha.
     Kwanciya sukayi kan gado.
   Bara nayi miki massage princess kai ya hafsa nice princess din.
     Sosaima kuwa kinma fi princess agurina.
     Ahankali ta rinka danna mata kafarta da jikinta.
    Itama taji ddi sosai saida ta tuna da mamansu lokacin da suke mata ita da Shaheeda suna dariya.
    Hawaye ne ya gangaro mata a haka Har bcci ya dauketa.. 
      Saida hafsa taga tayi bacci sannan ta matsa kusa da fuskarta tana da dakallanta.
     Ta kara fari duk ta fada fuskar tayi fayau dama ba Makeup take ba.
      Addu'a tayi musu sannan ta safe jikinsu da ita...☺


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
   01 Amal fansclub  💅🏻🌷


Written by Zeenaseer😘
[14/1 12:54] Zeeenaseeer: 🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
              👑👑
                🌳
      MARAICHI❣
           NA
  Zainab Naseer Sarki
      (Zeenaseer😘)


1⃣4⃣


🌺🌺
    I dedicated dis  page to u Anty Rabi'at,Ur d most special person in my life.ur my philosopher,guide nd lot more.wishing u all d season's happiness dis heartfelt can bring!.
  Lov u more nd more Anty Rabi'at.
                             🌺🌺


⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
........{7:30am}.........
     Fahad ne ya fito sanya cikin suit ash da red tie.yayi kyau sosai.
   Baiga kowa cikin falonba yasan bata tashiba kansa kawai ya girgiza dan baimasan yanda zaiyi da itaba.
    Nan inda flask din jiya ta yarda shi nan ya tanda shi,shikuwa sauri yake famanyi dan bazai iya bata lokacin saba.
    Fita yayi tare da kullo kofar falon da sauri yake yi.
 

   Bai jima da fitaba itama ta fito tasan ko ba'a fadaba ya fita.
Zama tayi kan kujera tana kallan yanda falon yiyi mugun dirty amma ita bazata iya gyara shiba dan gani take aikin yafi karfinta.
    Mikewa tayi ta nufi kitchen ta Dora abunda zatayi breakfast.
   Bayan ta gama karyawa ne ta shiga toilet ta tsan tsar kwalliyar ta.sannan ta dau key din motarta dan tana da gurin zuwa.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
   Bayan sun idar da sallah komawa sukayi suka kwanta dan yau hafsa bazata makaranta ba.
    Sapna kuwa wanka ta shiga nan danan tayi kayanta ta gama ta fito ta shirya cikin uniform din ckul dinsu.
   Hafsat ce ta dauko mata breakfast dinta sannan ta sanyata agaba da saita cinye dan taga kwana biyu batasan cin abinci gashi duk ta rame..
    Tana ci suna dan taba hira Har ta koshi sannan hafsa ta dauko kudin makarantar ta tabata dan dama Dan Asabe ke nawa kowa nashi sai tabama hafsa ta ajje mata.
  Sallama ta mata sannan ta fito ta nufi waje dan dama tun tuni Umma ta hanata gaisar da ita.
    Cikin mota ta shiga daga gidan gaba dan Safiya ke zama baya.
Kai tsaye makaranta aka nufa dasu tunda suka tafi babu wanda yake magana cikin motar sai karan radio da take tayi.
     A haka Har suka isa.
Bayan sun nufi class dinsu da yake class daya suke.desk dinsu ta nufa ita da kawarta Husnah.
    Bayan ta zaunane Hausa ke tmbyrta ya jikin nata.
    Da sauki tace da ita.
   Wai nema ke damun ki.
   Hmmm! Kawai dan Ciwan cikine.
   Allah ya sauwake ko de kema abunne yazu ta fada cike da zolaya.
   Kede kika sani koma me nene.
    Hahahhaa nasani ko kawar tawa ta girma.
    Toh bashi bane kawaide banajin ddine.
  Murmushi tayi tareda fadin jiya an bada Assignment ne.
  Aa Wallahi ba malamin daya bada..
  Yawwa Har naji ddi.


  Nan suka fara darasi Har zuwa lokacin da aka tashi tara.
     Suna zaune cikin class ita da Husnah da yake Sapna batasan hayaniya shiyasa bata fita tara.sunata hira suna dariya abunsu.
    Wata kawar safiyace ta mike tare da fadin hmmm ai duk wanda kaga baya fita break toh munafikine ko barawo.
   Ita de Sapna tasan dasu ake amma taki kulawa,Har Husnah zatayi magana tayi mata nuni da tabari dan Allah.
    Ywwa kuma Wallahi safiya muka nemi abunmu muka rasa Wallahi sai an biya mu.
    Husnah data kasa hakuri tace idanda ubanda ya isa ya hana sai mu gani.
Waya sanima ko kune barayin.
    Safiya ce tace ke Husnah badake mukeba saboda haka babu abunda ya dameki..
    Damu kuke mana su waya cikin ajin ko angaya muku munajin tsoran kune.
    Tasowa suka yi aikuwa itama ta tsalako ta nufe su alamun za'a ayi fada kenan.
    Sapna dake rubuta ta mike tare da fadin dan Allah kuyi hakuri munji mune amma kr kuyi fada pls.
     Banzaye marassa karfi safiya ta fada.
    Sapna ki rabu dani na koyawa yara hankali.
    Littafin ta ta dauka tare da fadin nina bar muku class din.
    Nan kuwa suka matso dama Husnah karfi gareta nan akahau fada harta basama Safiya baki.
    Nan aka kai kara gurin Auntynsu ta dau mataki sannan ta yima Safiya duka dan itada kawarta ne masu tsokana.

     Duk da safiya bataji dadin abunda ya faruba.gaba daya tunanin ta yana gida krtayi mata sharri a bugeta.
      Koda aka tashi da me daukar su yazo haka suka shiga gaba daya jikin Sapna yayi sanyi dan tsoro ji take kamar a yardata kan hanya.
     Da wannan tunanin Har suka iso gida.
   Da sauri Safiya ta shige gida tana kuka.
  Gaba daya hankalin Sapna ya tashi dan gaba dayama da ker take iya daga kafarta harta shigo gidan kasa hucewa tayi ta tsaya bakin rijiya tana rabe rabe.

     Tana shiga ta yarda Jakarta ta fada kan Umma tana kuka.
   Lafiya yar lele waya tafaki.
   Da gudu tayo waje tana fadin saina kasheta dan uwarta tunda tasa aka bugeni.
     Da sauri Umma ta biyota tana kiranta.
    Itama hafsa dake zaune a falo taji kamar karan kuka ya sanyata fitowa.

      Tana tsaye bakin rijiya ta anje jikarta kusa da kafa funta tana hawaye tana kallan kasa.
     Tana kara sowa da gudu ta turata baya.
Nan santsi ya kwasheta kanta ya bugu gaba daya ta fada cikin rijiyar.
    Wani irin ihu hafsa ta buga tareda yowa wajan da gudu.


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fansclub 💅🏻🌷


Written by Zeenaseer😘
[14/1 12:54] Zeeenaseeer: 🌳🌳        ⚜      🌳🌳
🌳                              🌳
              👑👑
                 🌳
       MARAICHI❣
              NA
  Zainab Naseer Sarki
      ( Zeenaseer😘)


1⃣6⃣


     .....I dedicated dis page you people 😘😘😘
Dimples Hamagee,sadnas,momsultn,mmnwalid,Preety Queen, ummieJ,mmnsudies,leecy,feeyah,Billy garladanchi,FIDDY G,Aisha bulkachuwa,miemiebee,Aunty jidderh,jiddah❣
Happiness is lyk butterfly,u run after it,it keeps flying away.if u stand still it comes &sits on ur shoulders.I wishes u happier moments ever❣
   Allah ubangiji ya kuma dau kakaku ya saka muku da JANNATUL FIRDOUS💋
    And always remember Zeenaseer lovs u nd support u❤



⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
     Daganan kai tsaye gidan malamin suka nufa nan ya tabbatar musu da mukatarsu ta gama biya.
    Haka Umma ta dawo gida cikin farin ciki dajin ddi.


Bayan 3hrs.
  Har lokacin dan Asabe yana cikin asibitin dan gani yake inya tafi za'a aiko mai da sakon mutuwar Sapna dan yama Riga yadau alkawarin babu wanda zai sanar da wannan al'amari.
    Hafsa ce ta fara bude idanunta tana kalan dakin cike da mamakin ganin ta cikin sa.
   Ahankali ta mike zaune tareda dafe kanta idanunta a rufe.
 Ido biyu sukayi da dan Asabe dake zaune kan kujera.
    Kara matsowa kusa da ita yayi tare da fadin sannu hafsa.
  Kai kawai ta iya dagawa.ahankali ta bude idanta daya kada yayi jajir murya na rawa kamar wacce zatayi kuka tace yaya Sapna ta mutu ko?
   Ta karashe maganar hawaye na zubowa daga idanunta.
    Ki kwantar da hankalin ki hafsa ki kwanta ki kuma hutawa.
    Tana kuka tana fadin amma yaya ya hankalina zai kwanta banasan wani Abu ya faru da ita dan Al.....
Kukanne yaci karfinta shiyasa ta kasa maganar.kuka taci gaba dayi.
    Shi kansa ji yake kamar ya fashe da kukan ya hutama zuciyar da yanda yakeji a yanzun.
    Da ker ya iya dafa kafadunta tare da fadin kiyi shiru Hafsa kibar kuka Allah shine maganin duk wata matsala. In......
    Wani iri yakeji cikin ranshi kasa karasa maganar yayi fita yayi daga dakin tare da janyo kofar.
    Jikin bango ya samu tareda dafa hannayansa gaba daya bayajin zai iya barin Sapna gurin danjin mahaifiyar ta yake tunanin maidata yana ganin nan ne kadai zata samu kulawa.
     Guri yasamu ya zauna dan gaba daya zuciyar sa ta dagule yanjin wani irin canji tattare dashi.


    Yana fita ta dago da kanta da jajayan idanunta duk hawaye ajikinsu.
     Waigowa tayi ahankali tana kalan Sapna dahar lokacin take kwance saman gado idanunta arufe tana bacci.
    Tausayinta hafsa keji sosai kamar tabdauke ta gudu da ita tabar gidanma gaba daya.



Bayan wasu yan lokuta.
    Ahankali itama ta fude idanunta tana daga kwancan dan bata motsa ko inaba ajikinta.
    Dakin raketa kallo ahaka.
  Hafsat ce ta fito daga cikin toilet ganin idanun Sapna abude yasa ta karasa wajanta.
   Zama tayi kusa da ita tana mata murmushi.
  Itama murmushi take yimata hawaye na zubowa ta gefe da gefan idanunta.
     Itama hawayen ne ya fara zuboma hafsa.
   Ahankali Sapna ta dago da hannunta ta fara share mata hawayan tana girgiza mata kai alamun tadena kuka.
    Hannun nata ta reke tare da hadewa da nata.
    Juyar da kanta tayi dayan gefan gadan tana kuka itama maras sauti.dan ita ji take tama gaji da rayuwar gidan gaba daya dama Allah zaisa ta mutu da ta koma wannan gidan.
    Dan Asabe ya shigo dakin da sallamarsa dauke da leda.murmushi ya sakrma Sapna tare da fadin sannu kinji.
   Kai kawai ta iya gyada masa dan batasan yin magana.
   Yaowa hafsa ga abincinan sai kuci kinga yanzu dare yayi saikuma da safe zanzo in Allah ya kaimu.
    Toh yaya saida safe.
Harya kai bakin kofa zai fita kafin.
    Ahankali ta firta yayah ka gaida gida Amma dan Allah kar agayama Shaheeda abunda ya faru.
    Batareda yace komaifa kawai ya fice tareda ja musu kofar.
    Sapna tashi kici abincin kinji ga magani nan da aka bada kisha.
   Hafsat ce ta taimaka mata ta mike zaune tare da sanya mata pillow abayanta.
    Ahankali ta dauko abincin ta shiga bata tana ci itama.
Tanayi tana bata ruwa harta fara koshi.
    Ya hafsa na koshi kema kici.
    Toh amma kema kidan kara mana ko yayane.
   Idan na kara amai zanyi.
    Toh bara nagama na taimaka miki kije toilet din ko?
    Gyada kanta tayi tana murmushi tareda jinginar da kanta jikin gadan tana kallan hafsa dake cin abincin.

   Tana gamawa ta kaita toilet tayo fitsari da alwala.
  Sallah tayi sannan ta kwanta lullube ta hafsa tayi da blanket tareda manna mata peck a goshi sannan tace gudnyt cwthrt.
    Murmushi tayi batare da tayi maganaba ta kuma kudindunewa dan sanyin da takeji.
   Komawa gadanta tayi itama ta kwanta.


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
   01 Amal fansclub 💅🏻 🌷


Written by Zeenaseer😘
[14/1 12:54] Zeeenaseeer: 🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
              👑👑
                 🌳
      MARAICHI❣
            NA
   Zainab Naseer Sarki
       (Zeenaseer😘)


1⃣5⃣

°°°°° dis page goes to u my lovely Ummie Khaleel💝
       Our frndshp ix lyk playing on see-saw,not only b cous its always fun wit u,but also b cous I wouldn't mind going down 2 c u
       Raising!!!❣
     Rwwly appreciate ur Lov nd care to me Bea.
     Iov u muah......💋😂


⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜

Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un!!!
   Take ta tambata tare da karasowa wajan da gudu tana kuka.
      Cikin rigiyar ta leka dan bamata iya hangota sai kyallin ruwa.
    Kamar mahaukaciya ko dankwali babu akanta tayi waje da gudu tana naiman taimakon mutane.
 
    Ita kuwa safiya jikinta yayi sanyi danta tsorata.Umma ce tajata cikin daki batare da ta furta kalma dayaba.
     Da sauri suka shigo gidan ita da wasu maza au uku.
      Dan Allah ku taimaka kar ta mutu ku dauko ta dan Allah.
   Kiyi hakuri kibar damuwa yanzu za'a cirota insha Allah karkiaamu damuwa.
    Dayane acikinsu ya fita.
    Gaba daya ta rude idananunta duk sun fito sunyi Jah.
    Da gudu tayi hanyar dakin Umma tana shiga ta shaki Safiya.
    Wallahi kema inde Sapna ta mutu saina kasheki.
     Ummace cikin tsawa tace baki da hankali hafsa anya ba asirceki akayiba yr uwar taki kike ikirarin kashewa.
      Itama yar uwa tace kuma wallahi ko badadi ko bajima sai Allah ya saka mata.kuma mundun ta mutu wallah saina kashe Safiya saide nima a kasheni.
     Sannan ta fito daga cikin dakin da gudu tanufi wajan rijiyar.
     Mutun biyune suka kara shigowa cikin gidan daga ganin daya kasan shine zai shiga cikin rijiyar tunda hannunsa rike yake da igiya kuma ya daurata a kugunsa da wani Abu kamar katifa.
     Sannan daya daga cikin su yace da hafsa gashinan ansamu wanda zai shiga ya fito da ita.
     Toh tace kawai sannan ta nufi daki da sauri ta dauko wayar ta jikinta sai faman rawa yakeyi.
    Daker ta iya samo numb.Dan Asabe.
   Ringing daya zuwa biyu ya daga.
     Yana dagawa ta fashemai da wani irin kuka.
    Lafiya hafsa menene ya fauru ki nutsu ki gaya min.
     Yaya Safiya ta kashe Sapna yaya ka taimaka da shiga uku.
     Shima salatin ya saki tare da fadin wani irin kiaa kuma ganin de zuwa.
    Sannan ya kashe wayar.
     Anyi sa'a mutumin ya shiga cikin rijiyar,bai dau lokaciba ya lalabota dan bata motsi ko kadan da alama suma tayi.
    Nan akahau janyo su cikin lokacin dabai huce 30 ba aka fito da ita.
    Fuskarta duk jini.da sauri hafsa ta karaso wajanta tana tanata tare da fadin Sapna dan Allah ki tashi karki mutu dan Allah.
    Daya daga cikin sune yace ki matsa kiyi hakuri bara a duba agani idan tana da rai.
     Gefe ta matsa tareda Dora hannunta aka tana rukwan Allah sai faman dafa da marwa take a tsakar gidan.
    Cikinta aka hau dan nawa ahankali kuma yana Murza mata kafafun ta.
       Sunyi harsun gaji Amma ko tari batayi.
      A sanyaye ya kalli hafsa tare da fadin mude munyi iya yanda mukeyiwa mutane.amma bata farka ba inaga saide kuyi hakuri gaskiya yarinyar nan ta rasu dan tasha ruwa dayawa sosai.
      Kawai gani sukayi itama hafsa ta yanke jiki ta fadi.
    Salati sukayi tareda matsowa gaf da ita.
  Daya daga cikin sune yace wai ba kowa cikin gidan nan ne.
   Inaga da mutane mana.
    Dallah mutan gidan nan mana au fito suga abunda ke faruwa mana.
     Shiru ba amsa suka fara kallan kallo tsakanin su.
     Ko sallama baiyi ba ya shigo cikin gidn dan gaba daya hafsa ta tadamai hankali.
    Lafiya ya tambayi mutanan daya gani.
    Nan suka yimai bayanin kosu suwaye.
   Hafsat ya dauka sannan yace su dauko Sapna su sakota cikin mota dan Allah.
    Nan aka sanyasu cikin mota sannan ya sallami mutanan nan yaja mota yayi asibiti dasu dan gab daya shima hankalinsa yayi mugun tashi.
     Yana zuwa aka an anshe au akayi emergency dasu.
    Yana nan tsaye sai faman safa  da marwa yakeyi.
     Har ya gaji da tsayiwar ya zauna.
   Can bayan lokuta saiga nurse ta kirashi likita nasan ganin sa.
    Mikewa yayi dan gaba daya hankalinsa atashe yake.
    Bayan sun gaisa ya nunamai kujera ya zauna.
    Amma Alhmdullh, dukkan sun farfado Amma ita yarinyar tana bukatar Hutu.
    Ita kuma dayar ko zuwa anjima zamu iya sallamar ta.
    Ahamdala yayi tareda godema Allah da kuma likitan.
    Sannan yace zan iya ganin su.
    Ba damuwa muje.

Tare suka fito gasunan akwance ko wacce ansamata drip.
  Duk bacci sukeyi.
Sai yanzu dan Asabe ya lura da ramar da Sapna tayi abun tausayi.
 

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
      Tafdijan ni za'a ma iska cin Umma ta fada sannan tace da Safiya ta zauna zataje yanzu zata dawo.
     Gidan kawarta ta nufo.Hansai.
    Tana shiga ba kowa tsakar gidan sai dakin ta shiga.
    Aa yau Hauwa ce gidana dama baki nai mana saita baci.
    Hmmm kede bari Hansai.ni za'a ma lalata wai arabani da daya ta.
    Toh nikuma Allah daya saina raba Sapna da kowa nata sai kowa ya kita.can danjin uwar tama so nake su manta dasu ita kuwa hafsa da dan Asabe sutsaneta su dena kula ta.
    Wannan shine burina saboda haka yanzu ki tashi mutai wajan malam dabansan bata lokaci.
    Ahaiiiiye kinji uwar bari ai dama na hidi maki,dan kin kawar da uwarsu baki komiba irin wadan nan mugun iri ke garesu tas ake hulankanta yan isa.
    Kwashe sukayi da dariya.
    Shiyasa nike sanki kawata baki wasa.
    Sosaima kuwa danni Wallahi kishiya bata isaba ko ita wace balle yayanta.sudin banza,
    Innice cikin gidan nan bamaicin gadan mijina dagani sai diyana.


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
   01 Amal fansclub 💅🏻 🌷


Written by Zeenaseer😘
[14/1 12:54] Zeeenaseeer: 🌳🌳      ⚜         🌳🌳
🌳                              🌳
              👑👑
                🌳

1⃣7⃣


°°°°°°°°{6:42am}°°°°°°°°
   Hafsat ce ta farka dan gabatar da sallah asbah.bayan ta idarne ta tashi Sapna itama tayi.
   Bayan sun idarne kwawacce ta koma ta kwanta sai 10am suka farka Sapna ce ta fara tashi dan tsananin yinwar da takeji.
    Ahankali ta mike ta shiga toilet tayi wanka sannan ta fito ta maida kayan jikinta danma Allah ya taima keta period dinta kwana daya yayi ya dauke.
    Komai bata shafaba tunda babu abunda aka kawo musu.zama tayi ta kunna TV tana kallo.
    Hafsat ma tashi tayi sannan ta kalleta tareda fadin harkin tashi kenan.
    Eh wallah kuma Har wanka nayi.
    Wanka kuma keda kifa fada rijiya aina zata sainan da irin 2wks dinan zakiyi wanka.
   Dariya suka aa gaba daya.
   Sannan ta mike tsaye tana fadin kinga yaya Har yanzu baizoba koma kuma nasan kinajin yinwa ko?
    Eh ta gyada kanta.
  Bara nima na dan watsa ruwa amma kamata yayi ace yazo.
   Bata jima da shiga toilet dinba.aka turo kufar.likita ce mace da nurse suka shigo dakin.
   Zamatayi kan kujera tareda kallan Sapna tana murmushi. Sannu yan mata tace ya jikin.
   Da sauki Sapna ta bata amsa.
   Masha Allah amma yanzu babu inda yake miki ciwo.
   Eh babu kaina ne kawai yake dan min ciwo lokaci zuwa lokaci.
   Toh insha Allah shima zai dena inkinasan maganinki yanzu mun sallameku zaku iya tafiya inna yar uwar taki.
   Ammm tana toilet amma yanzu za...
    Bata gama rufe bakintaba ta fito daga toilet din tana yafa veil din kanta.
   Gaishesu tayi sannan ta zauna.
  Ya saukin jikin likita tayi mata sannan ta gaya mata cewar an sallamesu kuma ta bata sauran magungunan Sapna.
   Godiya tayi musu tareda fadin dan Allah ko zaki bani aran fone dinki kinga Har yanzu ba wanda yazo daga gida ko lafiya.
    Ohk ba damuwa hannun ta tazira cikin aljihun rigarta ta dauko tare da mika mata.
   Sannan ta mike tace inkun gama saiki kawomin cikin office dake kallan dakin ku.
   Toh nagode ta masa sukuma suka fita.
    Numb.dan Asabe ta kira amma yaki dauka karshema akashe gajita tayi mutukar mamakin hakan.
    Haka Umma ma da taki kira shiru ba'a dagaba dan haka saita kira Jameel saurayin dazai aureta.
    Bayan sun gaisa take sanar masa cewa itace suna asibiti yazo ya maidasu gida dan Allah dan haryanzu gida shiru kuna ta kira ba'a daukaba.
    Ohk ganinan zuwa inka karaso saika kirani.
   Sannan ta katse wayar.
 
    Basu jima da gama wayarba ta kuma jin ya kira ta.
    Sallama tayi tare da karawa a kunuwanta.
    Yauwa kufito gani nan na iso koba asibitin da kuke zuwaba.
   Eh Shifa gamunan.
 Sannan ta mike suka fito daga dakin.
  Knocking office din Dr.sukayi tare da shiga ta kuma yimata godiya ta bata wayar,sannan suka fito.
    Da yake tasan motarsa can nesa ta hangoshi sannan suka tako Har zuwa wajan.
    Da sallama suka shiga cikin motar hafsa gaba ta shiga ita kuma Sapna tana baya.
    Gashe shi tayi cikin fara'a ya amsa yana kallan ta ta mirror.
    Sannan yace waye bashi da Lafiya ne? Ya fada tare da yima motar key.
    Wallahi Sapna nace batajin ddi shina mukazo jiya aka kara mata drip yanzu kuma suka sallamomu.
     Ohk Allah ubangiji ya kara sauki ya fada idansa kan titi.
    Suna tafiya suna hira itade Sapna tana daga baya abun duniya duk ya isheta dan ita Har batasan Shiga cikin gidan.
    Basu jimaba ya suka karaso gidan.
A kofar gidan yayi parking da motarsa sannan sukayi sallama dashi suka shiga ciki.
     Da sallama suka shiga gidan,dakinsu Sapna ta nufa ita kuwa hafsa kitchen ta nufa dan samun abunda zasuyi breakfast dashi.
   Tea ta hada musu sannan ta dauko bread ta kawo musu sukaci suka koshi.
     Sannan Sapna ta shiga daki ta cire uniform din nata ta sanya kayanta marassa nauyi ta haye gado ta kwanta dan tan bukatar hutawa.
     Ita kuwa hafsa gaba daya ji take zuciyar ta kamar wanda aka matama rai duk haushi takeji kuma ba haushin kowa takeji ba inba na Sapna ba bama tasan ta ganta kusa da ita.
    Tsaki tayi tare da mikewa ta bar dakin.
    Dakin Umman ta tanufa.baga kowa cikin falonba dan tasan safiya na makaranta. Cikin dakin ta shiga.
    Umma na zaune gefan gado.
    Gaisheta tayi tareda fadin Safiya na makaranta ne.
    Eh tafada sannan tace yame jikin?
   Kai Umma nikuma ina ruwana da wata me jiki ita ta sani sannan ta mike tabar dakin danji take kamar ta kashe ummar datayi mata maganar sapnar.
    Dariyar mugunta ummar tayi tare da fadin yanzuma aka soma wasan harni za'a ma iya shege.
   Hahahhahahahha ta kuma kyalkyalewa da dariya kamar mahaukaciya.

ALLAH SARKI SAPNA 😢😢😢



😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
  01 Amal fansclub 💅🏻🌷



Written by Zeenaseer😘
[14/1 12:54] Zeeenaseeer: 🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                 🌳
      MARAICHI❣
               NA
 Zainab Naseer Sarki
      (Zeenaseer😘)


1⃣8⃣

      Pls kuyi hakuri kwana biyu ina busy ne amma insha Allah zanna kwari ko pg 1 narinka post.
     Lov u so muah....💋


⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜

     Falo hafsa ta koma ta kwanta saboda zuciyarta dake faman tafasa kamar wadda aka yima wani Abu.
      Rasa meke mata dadi takeyi dan kwata kwata batajin ddin hakan.

    Bacci sosai tayi dan tana bukatar hakan kusan awa biyu ta dauka tana  bacci sannan ta farka.
Ahankali ta mike ta nufi toilet dan yin azhr.
Bayan ta idar da sallah ne ta fara jin yinwa.
   Mikewa tayi ta nufi dakin Umma dan taga kamar hafsa bata nan.
  Da sallamar ta ta shiga dakin amma babu wanda ya amsa mata.
   Ganin hafsa zaune ta hade rai.ya sanya Sapna kin karasawa wajanta daga bakin kujera tace ya hafsa yinwa nakeji.
    Wata harara ta galla mata tare da fadin bari na zama abinci saiki cinyene.waye jakinki acikin gidan nan dazai zauna yana dafa miki abincin.
    Ahankali ta mike cike da mamaki.Umma ta kallah daketa faman murmushi.
  Haka ta fito daga dakin kamar kazar da kwai ya fashema aciki.
    Dakinsu ta zauna saman kujera tare dayin tagumi dan gaba daya abun ya fata mamaki.
    Kallan jikinta tashiga yi tare da fadin aikuwa me garine da bbu me sona.yanzu itama Hafsat ta dena sona.
Ina akesan na sanya kaina wannan wata irin rayuwa ce.
   Fashewa tayi kuka me kara.dan gaba daya tagaji da zaman duniyar dama ta mutu ta huta.da wannan bakar rayuwa da take fuskan..
   Yanzu kowa baya kaunarta inaga nan gaba idan ta kuma girma.
   Kukan da takeyi ne taga bazai yimata maganin yinwaba ya sanya ta mike daga zaunan da take ta fito ta nufi kitchen.
   Babu alamun abinci.gashi gabadaya bata Jin dadin jikinta.
   Dabarace ta fado mata.
 Fitowa tayi daga kitchen dinta ta sanya hijab dinta da takalmi ta nufi gidan Aunty Naja.

    Da sallamar ta tashiga cikin gidan.jin shirun kamar ba kowa ya sanyata nufi dakin.cikin falon ta shiga shima ba kowa.
    Zama tayi kan kujera tana kalle kalle dan tasan tana daki.
    Bata jimaba sai gata ta fito.
   Murmushi sukayima juna.sannan Sapna ta gyadata.
   Lafiya qlau Sapna kwana biyu ko lekoni bakyayi nasan da Shaheeda na kusa ko dayaushe tana tare dani.
   Hmmmm! Wallahi Aunty ba haka bane banajin ddi ne kwana biyu amma yanzu jikin da sauki.
   Allah sarki kuma baki sanar dani ba.Allah ya sauwake.
   Ameen Ameen kawai ta fada tayi shiru dan tanasan tam bayarta abinci kuma tana tsuran kar tayi tunanin ko bata ci agida.
    Babu de matsalar komai Sapna.
   Ta fada tareda dafa kafadarta tana kallan fuskarta.
    Hmm! Wallahi Aunty bbu komai kawai de inasan ki zubamin abincine a gida macaroni suka dafa nikuma bana sanshi.
    Toh ta fada tare da mikewa dan tanajin tausayin sapnar.
    Bata dau lokaciba ta hado mata abinci mai rai da lafiya da ruwa da juice.
   Ta zauna tare da bismillah ta fara ci suna taba hira sama sama harta cinye duka.
Tasha juice din sannan tace Aunty dan Allah kiyi min kitso kaina ya jima ba kitso.
    Toh Sapna gama cin abincin.
    Kai Aunty na koshi wallahi ai naci dayawa.
   Aa kiri kokari ki cinye sai in miki kitsan.
  Da ker ta iya cinyewa sannan ta kwashe kwanikan ta gyara wajan.
   Saida sukayi sallah suna hira sannan sukayi sallar la'asr din.
    Sannan ta fara yimata kitsan.

  Sunayi suna hira har suka gama tayi mata kitso me kyau.
  Sannan gyara gurin Aunty Naja nata yaba kyan kitsan.
    Saida ta tsareta taci abincin dare bayan magrib sannan ta fito ta nufi gida.

    Tana ta faman sauri kar ayi mata fada.tana shiga sukaci karo da Abba a soran gidan.
   Da sauri ta matsa baya tana dafe kanta.
   Daga gidan ubanwa kike.
  Da baya ta fara jah dan tasan bashi da imani zai iya dukanta.
   Da sauri ya wartota tareda shigo da ita cikin gidan Har dakin Umma ya zaginta.
 

😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fansclub 💅🏻 🌷


Written by Zeenaseer😘
[16/1 12:40] Zeeenaseeer: 🌳🌳       ⚜        🌳🌳
🌳                              🌳
              👑👑
                🌳
      MARAICHI❣
              NA
 Zainab Naseer Sarki
     ( Zeenaseer😘)


1⃣9⃣

   A tsakiyar falon Umma ya jefar da ita.
Da sauri ta mike ta fara ja da baya tana hawaye.
   Umma da ke zaune a falon ita da safiya suna kallansu da mamaki ita kuwa hafsa dama tana cikin daki.
   Daga gidan ubanwa kike.
   Kamar ta mutu dan tsoran shi murya na rawa tace daga gidan Aunty Naja nake.
   Ummace ta juyo tana kallanta kafin tace daza ki fita wa kika tambaya kodanmu kin raina mu kuma dan ace bama kula dake ki jamana zaji.
   Kanta take girgizawa tare da fadin wallahi Aa dan Allah Umma kiyi hakuri wallahi bazan kara fita ba tareda iznin kiba dan Allah ta karasa maganar tareda durkusawa hannunta biyu a hade.
    Shiru falon yayi sai karan kukan Sapna akeji kasa kasa.
    Abba rabu da ita karmu karasa gawar daba tamuba.
 Ke kuma tashi ki bamu guri.
   Da sauri ta mike ta rabe ta jikin bango ta fice daga cikin dakin da gaba daya ta rude.


   Tana shiga daki ta shige ciki tareda fadawa kan gado dan gaba daya bata kaunar rayuwar gidan nan.
   Kuka tasha sosai sannan ta mike tayi sallar ishsha.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
  Tana kwance saman gadanta da alama bacci take shirin yi.
  Fahad ne ya turo dakin da sallamar sa.
Sannan ya kwanta a bayan salma tare da janyota jikinsa.
Kiss ya manna mata a huya,kafin ya furta mata salma!
   Idanunta a rufe ta amsa masa da uhmm!
   Pls ki taimakamin kisan ina kokari dake.
   Gaskiya fahad banajin ddi kuma kaima ka sani.
   Amma ai cutanki bazai hanani biyan bukatana naba ko.
   Nide kayimin uziri ka bari na kara samun sauki tukun.
   Toh yanzu ya kikesan nayi tana maganar yana kissing dinta.
   Janye jikinta tayi daga nasa sannan ta gyara hannun rigarta.
 Haba Fahad sai kace baka tau sayina.
   Ba haka bane salma kabanki ke miki ciwo kuma naga da sauki yanzu ya kikesan nayi kenan kuma yaushe raban da kibani hakkina.
    Gask......bata karasa maganar ba yayi saurin matsowa kusa da ita tare da sanya bakinsa cikin nata.
   Tana turesa alamun bata so amma yaki sakinta.
    Tana kuka tana dukansa da yakushinsa Har ya biya bukatarsa sannan ya mike ya bar dakin.
   Kuka sosai tasha sannan ta mike ta nufi toilet dan gyara jikinta.
   Shima dakin shi ya nufa yana tsaki dan jin haushin abunda salmar ke yimasa.yayi wanka ya kwanta.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
   Tana tashi tayi sallah wanka tayi sannan ta shirya cikin kayan makarantar ta.
     Dakin Umma ta nufa,da sallamar ta tashiga suna zaune suna yin breakfast.
   Daga wajan kofa ta durkusa tare da fadin Umma ina kwana!
  Ba yabo ba fallasa a fuskarta ta amsa da lfy.
    Sannan ta dubi wajan hafsa da tun shigowar Sapna ta janza fuska tace ina kwana Anty hafsa.
   Harara ta wurga mata tareda fadin danvan  kwanaba zaki ganni.
   Kanta a kasa ta mike tabar dakin ta koma dakinsu.
    Cikin inda ummata ke anje kudi ta shiga dubawa dan yanzu taga ko kudin makaranta da ker in zata samu.
Cikin sa'a kuwa taga akwai kudi ba laifi.
   Naira50 da dauka ta fita kafin me daukarsu yaxo ta nufi inda ake saida kosai ta siyo ta boye kayanta ta shige daki ta cinye tasha ruwa.
    Sannan ta fito dan taji kamar anzo daukarsu.
     Haka ta nufi motar inda ta saba zama bayan ta gaida driver n nasu.


⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
    Bikin hafsa ya matso gida ya fara ciki da yn uwa da abokan umma  sai faman hidima ake.
    Dan harsun Nana ma sun dawo gida dan tare za'ayi bikin naso.
  Anata faman shagali itama Shaheeda an kawota.
    Sapna kuwa kamar me aiki kullum sai yamma take wanka sai faman aiki take.
    Ko kunshi bata samu anyi mataba ballantana kitso.
   Haka taketa yawanta duk inda tayi Shaheeda na biye da ita.
     Haka akayita gudanar da bikin Har ranar daurin aure.


  Ranar daurin aure akayi yini agidan sannan aka rankaya daukar Amarya. Nana katsina aka kaita ita kuwa hafsa nan cikin kebbi.
     Wqshe gari yn bikin duk sun fara tayi gida jansu dan yanzu gida ya koma daga Umma sai Sapna da safiya.
    Nan aka cema safiya ta koma dakin su Sapna ya zama dakinsu su biyu.
    Hakan kuwa akayi amma Sam safiya bata barin  Sapna ta Hutu.


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
 01 Amal fansclub 💅🏻🌷



Written by Zeenaseer😘
[16/1 12:43] Zeeenaseeer: 🌳🌳       ⚜        🌳🌳
🌳                              🌳
              👑👑
                 🌳
      MARAICHI❣
             NA
 Zainab Naseer Sarki
     (Zeenaseer😘)


2⃣0⃣


BAYAN SHEKARA 3
 
   Su sapna an zama yn mata sosai dan yanzuma suna SS2 first term.
   Ta kuma kyau da haske duk da batajin ddin zaman gidan nasu haka itama safiyar.
    Hafsa tana da da daya ita kuma Nana tana da yara biyu.
      Har yanzu dangin Sapna basa nemansu kuda Naja taje gida tayi maganar yaran ba'a wani daukarta da mahimmanci hakan yana mutukar bata mamaki.
  Hakan inta nuna tana San taje da yaran su dan Asabe basa yarda.
   Haka take rabuwa dasu saide lokaci lokaci Sapna kan leka gidanta kuma ana kawo Shaheeda ma.

   Ita kuwa Rahama da mijinta Abba kullum suma cikin fada suke kuma Har yanzu taki haihuwa gashi ta raina Umma.
    Haka shima kusan kullum a bige yake shigowa gidan.
    Wani zubin  yana zage zage wani zubin kuma surutai.
    Itama Umma babu abunda ya canza daga halinta kullum cikin ta kurama Sapna take bata kaunar ko kadan taga taci gaba burinta ta zamo ci baya.
    Jin ddin sapna shine kawai ta tafi makaranta shiya aa kullum bata fashi tana samun hutawa.kuma kullum basa bata breakfast saide in taje makaranta kawarta Husnah ta kawo mata Har kudin makaranta take bata dan tana tau sayin kawar tata.


Monday mrng❣
  Da sassafe Sapna ta tashi kamar yanda ta saba dan yanzu Umma ta kori yn aiki ita keyin komai.
   Bayan ta gama aiyukanta sannan ta hada musu breakfast ta kai dakin ummar.
   Toilet ta nufa tayi wanka ta shirya cikin uniform dinta.
Sannan ta fito.
    Ita kuwa Safiya tana kwance saman gado dan yanzu kullum saita sanya sunyi late ko kuma a dukeso.
   Ahankali ta tsaya kusa da gadan dan ta tasheta.
    Fashi 8am ta kusa yanzu inta tashi tayi wanka,kwalliya, breakfast sai kusan tare tasan yau zasu tafi gashi yau dutyn Uncle John ne kuma mugune.
    Ya Safiya!! Ta fada ahankali sau biyu.
   Tana mikewa ta wanketa da mari.
  Ke wata iriyar jakace,wata iriyar kwakwalwa ke gareki na fada miki kada ki kuma tashina a bacci ko ban gaya mikiba.
   Hannunta akan fuskarta dan taji zafin Marin ta Shiga kada kai dan ta gaya mata.
   Kin gayamin amma dan Allah kiyi hakuri ki tashi ki shirya dan wallahi yau dukan late za'ayima.
   Akashemu kuma ni karki dameni banza kawai mutun yana baccinsa kin zo kin ta sheshi ta mike tare da bangajeta ta shige toilet din.
    Binta tayi da kallo sannan ta fice daga dakin.
    Waje ta fita driver na zaune cikin mota yana jiranau.
Dama shima ya saba da halin safiya shiyasa ma baya damuwa.
   Gaidashi Sapna tayi sannan ta zauna tareda fadin kaga Har yanzu shiru bata gama shiryawa ba.
    Hmmm! Rabu da ita komai ae lokaci ne,wlh nan gaba koda ance tayi bazatayi ba.
   Hakane Allah de yasa tayi maza ta fito dan bansan dukan late wlh.
     Saida suka kusa 1hr suna jiranta sannan ta fito daga cikin gidan sanye da kayan gida.
     Tana shiga cikin motar ta zauna.tare da fadin ka kaita makaranta ni unguwa zaka kaini.
    Cikin zuciyarta tace lallaima safiyar nan yr rainin hankali ce.dama tasan ba makarantar zata ba ta fatamin lokaci.
    Habu ka fara kaini unguwar saika kaita makarantar.
     Wallahi ni zaka fara kaiwa tunda nice zani guri mai mahimmanci ita ta tari napep ta tafi mana.
   Ni kike gayama wannna mafanar.
   Ai maganar gaskiya ne da kinsan bazakiba aisaiki fadamin amma kika zaunar damu tun dazu ina jiranki kuma yanzu ki fito kice ke za'a kai.
    Habu dan Allah muje ni ina kara yin late.
   Lallaima yarinyar nan ni kike gayama wannna maganar.
   Banza tayi da ita bata kuma tanka mataba.
   Fita tayi daga cikin motar shikuwa habu yaja motar ya tafi.

  Tana Shiga cikin gidan da kukanta.gurin Umma ta nufa.
   Tana toilet dan haka sai ta zauna tana jiran fitowarta.
     Bata dau lokaciba ta fito tana tsane kanta ganin Safiya zaune ya sanyata dakatawa tare da fadin lafiya kuwa naga kin dawo ko kin fasa tafiyar ne?
    Cikin muryar shagwaba tace waini za'a ma iskanci.
Wai habu cewa yayi saiya fara kai sapna sannan zai dawo ya kaini.
    Wata ashariya taja sannan tace motar ta uban shice da Har zai fadi hakan kaita yayi saide ta taho a kafa maga ubanda zai dauko ta.
Bani wayata na kira sa.

   Suna tafiya suna hira saura kadan ya karasa da ita makarantar.
Wayar shi ta fara ringing.
    Tunda yaga numb.Umma hantar cikinsa ta kada.
  Da sauri ya daga tare da karawa a kunne.
Barka da safiya hajiya.
    Habu ni zaka watsama kasa a ido.ka nunamin ban isa da gidana ba.
    Wallahi hajiya ba haka babe Ayi hakuri dan Allah.
   Toh da ka kaita da baka kaitaba ka dawo yabzunnan na baka 5mins Wallahi ka huce abakin aikinka.
    Bata jira cewar shiba ta kashe wayar.
    Da Sauri ya tsaida motar tareda kallan Sapna da tayi shiru tana sauraran wayar su da Umma.
     50ya mika mata tareda fadin ga shinan ki hau napep ya karasa dake sai nazo daukarki.
    Toh kawai tace dan bakinciki ji take kamar ta yi kuka.
    Sannan yaja motar da sauri sai can gidan.
     Napep tq samu ta shiga dan ya karasa da itama makarantar dan 9:43 am lokacin.


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
  01 Amal fansclub 💅🏻🌷



Written by Zeenaseer😘
[16/1 19:52] Zeeenaseeer: 🌳🌳        ⚜       🌳🌳
  🌳                          🌳
               👑👑
                 🌳
      MARAICHI❣
              NA
 Zainab Naseer Sarki
     (Zeenaseer😘)


2⃣1⃣


   Yana yin parking cikin gidan ya shiga da sallamar sa.
      Tana zaune kan kujera ga safiya na zaune itama tana facing kujerar Umman tata.
    Cikin dakin akamai izinin shiga.
   Yana shiga ya durkusa tare da fadin gani hajiya.
   Yanzu sabo da Allah habu abunda kayi ka kyauta.
Taya gamesan zuwa unguwa kace saika fara kai dan makaranta sannan ka dawo ka kaita.
Ubanme take fabimmata a makarantar.toh Wallahi ka kiyayeni babu abunda ya shafeka da wannan yarinyar duk abundavsafiya ta fada shine zaka bi.kuma yau karka sake ka dauko ta kuma ka sake ko a boye ne abakin aikinka.
Tashi kije ya kaiki.
   Toh hajiya insha Allah za'a kiyaye ki huta lafiya ya fada tare da mikewa at fita.
   Shi kansa yana mamakin abunda ake yima Sapna ganima yake kamar kowama ya tsaneta cikin gidan.
 

      Tana sauka daga kan nepep din ta mika masa kudinsa tare da fadin nagode.
      Ba kowa a kofar makarantar sai me gadi yana zaune da yr radion sa yana ji kusan 10am.
    Karasawa tayi gurin sa tare da gaidashi.da yake sun saba dashi nan ta tsaya tare da fadin baba Har an kule gate din.
     Gefe ta samu ta zauna tare da rufe fuskar ta da tafikan hannunta tana jin wani irin bakin ciki cikin ranta.
   Sapna ya akayi kikayi late haka ina yar uwar taki.
   Kwallar da zata fado ce tayi maza tayi kokarin maidata tare da fadin Wallahi babu wata yr matsala aka samu.
   Eyyah gashi kuma kinga ka kidar makarantar nan in aka kulle ba'a budewa sai an tashi.
   Batare da ta kalleshiba kanta a kasa tace na sani baba.
     Nan tayi ta zama ga yinwa da takeji dan ba wani Karin kirki tayiba.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
    Koda gari ya waye kin fitowa tayi daga dakin tayi zamanta aciki dan fishin da take da Fahad din.
    Shima kuma daya tashi ya gama shirinsa zai tafi office dakinta ya turo da sallama ya shiga.
    Tana kwance saman gado ta juya baya.
Ahankali ya karasa wajanta tare da zama gefan ta.
  Idanunta biyu taji lokacin da ya shigo amma saurayi banza dashi.
    Baby! Ya fada tare da matso da kansa kusa da kanta.
   Pls kiyi hakuri Wallah nima ba'a San rainaba hakan ya faru pls am sorry.
   Bata ce masa komaiba kawai kara rufe idanunta tayi.
   Pls I don mean to upset u,kawai lokacin I can't control ma self ko kinasan na rinka bin mantan waje ne.
    Da sauri ta mike tare da rungume shi tana hawaye.
   Goge mata ya shiga yi yana fada kiyi hakuri dan Allah barin sake ba insha Allah duk lokacin da kika ga dama am always ready.
    Murmushi ta sakar masa tare da fadin toh naji amma karka kara yimin da zafi.
   Ai bana miki da zafi kice kikaja yauma kinga nayi hakuri amma an dena.ya fada tare da hada kansa da nata.
   Hannunta ta sanya ta zagaye huyansa tare da manna masa peck a goshi tare da fadin I Lov u.
    Lov u too my soul..
Sannan ya mike yana daga mata hannu alamun bye.
    Shima hannun ya daga mata sannan ya fice zuciyarsa yana fadin babu aikin komai sai aukin San soyayya.
    Yana tafiya ta kuma mikewa saman gado dan yin wani saban baccin.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
     Tana zaune abakin gate Har aka fito break aka koma amma ba yanda ta iya.
    Saide ta dauko nvl ta karanta inta gaji ta maida tayi kalle kallen hanya wani tymdin sudan taba hira da me gadi.
    Tana nan zaune Har 2pm sannan aka tashi.
 Duk an anjinsu sunyi mamakin ganinta bakin gate wasu suce meyasa bata koma gidaba.haka de sukayita tambayarta itade saide tayi Murmushi.
    Husnah na ganinta ta rugo da gudu tare da rungume ta.
    Da mamaki ta kalleta tare da fadin ya baki shiga ba.
   Wallah late naxo kuma kinsan ba'a bude gate in 8am ta huce.
  Hakane amma ina safiya.
   Dama ita bata zoba saini daya.
    Zama sukayi kan wani bench sannan Husnah ta bude Jakarta ta dauko cupcake guda biyu da juice na kwali ta mika mata tace ga naki naci nawa.
    Murmushi tayi sannan ta rungume ta ta ansa dan wata iriyar bakar yinwa ta keji Har tadan fada.
    Nan ta amsa ta hau ci,kawar tata sai kallanta take kamar mahinwaciya saida ta cinye duk ta sanye juice din sannan ta kuma rungume Husnah rana kwalla tare da fadin.
    Allah ubangiji ya biyaki Husnah keda iya yanki da dukkan danginku da ma fificin sakamako da gidan jannatul firdous.
    Itama rungume tan tayi tana hawaye tare da fadin ameen Sapna.
   Janye jikinta tayi sannan ta fara guge mata hawaye tana fadin meye kuma na kuka Sapna ki barifa kinga duk ga mutanenan suna kallanmu.
    Hawaye ne yaci gaba da zuba a idanta sannan tace dolle nayi kuka Husnah tun mauna yara kike kaunata kuma gashi Har yanzu baki gazaba kullum dada kaunata kike.
    In uwana na jinima basamin qauter kaunar da kikemin,kuda ina cikin rashin jin ddi innazo makaranta sai kinyi kokarin sani farin ciki tata bazan gode mikiba.
 Wallahi banga abunda zaki bukata agurinaba in kasa miki shi koma menene.
    Da da rungume ta Husnah tayi tare da fafin nima nagode Sapna Allah ubangiji ya baki miji na gari wanda zai jiyar dake ddin da bazai taba karewaba wanda zai baki farin ciki Har abada.
    Ameen thumma ameen tace sannan tace kinga Har anzo miki.
    Toh sai gobe kinji Sapna ta ko zakixo mu kaiki gida.
    Aa nasan habu zaizo ki gaida au mami.
   Toh insha Allah zasuji sannan ta nufi motar su Har sukayi nisa suna dagawa juna hannu.


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
 01 Amal fansclub 💅🏻🌷



Written by Zeenaseer😘
[17/1 20:33] Zeeenaseeer: 🌳🌳        ⚜       🌳🌳
  🌳                           🌳
              👑👑
                 🌳
       MARAICHI❣
              NA
 Zainab Naseer Sarki
     (Zeenaseer😘)


2⃣2⃣


Tana nan zaune Har aka kira la'asr nan ta fara tunanin lafiya kuwa yau habu yakai wannan lokacin bai zoba.
    Gurin me gadinsu ta nufa yana zaune shima.
   Aa Har yanzu ba'a zo daukar kiba yafada da mamaki tana kallanta.
  Eh wallah bansan meya sanyaba.
   Toh! Ikon Allah amma baki da numb kowa da za'a kira a sanar musu me daukar taki Har yanzu bai zoba.
    Wallahi bani da numb kowa nasan zakayi mamakin ganin budurwa kamarni bata rike numb kowa a gidan suba ta karashe maganar tana murmushi.
    Gaskiya kam da mamaki.
   Yawwa baba dan Allah 10 zaka bani zansai ruwa ina jin kishi gashi ban fito da kudi ba.
    Hannu ya sanya cikin aljihunsa ya dauko mata ya mika mata.
    Dan durkusawa tayi ta amsa tare da fadin na gode.
    Nan ta nufi wani dan shago,ruwan ta siyo sannan ta koma ta zauna tare sa shanye kayanta.
   Duk tayi wani irin abun tausayi yarinyar kyakyawa amma babu gata.
    Har kusan 5pm tana zaune tagade abun bana zama bane.
   Tashi tayi tare da fadin baba bara na tafi gida sai gobe.
   Sallama yayi mata sannan ta tari napep ta shiga.
    Nan tamai kotancan inda zai kaita ya fada mata kudin ta shiga.
Nan ya nufi gidan da ita.

Suna karasawa ta fito tare da fadin bara na shiga na dauko maka kudin.
   Ba damuwa yace da ita.

 Da sallama ta shiga gidan.dakin Umma ta shiga da sallamar ta ganin hafsa zaune ya sanyata yin murmushi duk da hafsa bata santa amma ita Har yanzu bazata daina kaunar taba.
    Laaah ya hafsa sannu da zuwa.
    Ywwa ta fada ba annuri a fuskar tata Sannan tace sai yanzu zaki dawo daga makarantar.
    Wallahi habune bai zoba kuma na gaji da zaman jiransa shiyasa na dadi me napep ma na tara nace innazo gida sai abashi kudin.
      Ubanwa zai bashi kudin dama kin anje banki agida dole ki dauko me napep Umma ta fada.
    Shiru tayi dan dama tasan Umma bazata taba bada kudin nan ba koda zata mutu.
     Hafsa ma banza tayi da ita sukaci gaba da hirar su.
   Mikewa tayi kamar kazar da kwai ya fashema a ciki.
   Part din aunty Rahma ta nufa dan tana tunanin maybe zata iya bata.
   Da sallama ta shiga falon tana zaune kan kujera tana kallo.
    Aunty sannu da hutawa.
    Yawwa ta fada tana murmushi sai kallan ta take kamar mayyah.
   Ita kanta tana mamakin irin kallan da Aunty Rahma ke yawan yi mata.
   Lafiya Sapna na ganki da uniform yar yanzu baki cire ba.
   Eh wallah Aunty habu ne bezoba shine na tari napep kuma gashi bani da kudi sai yanzu na dawo.shine nazo dan Allah ki bani aran 200 wallah zan baki.
    Murmushi tayi na yn duniya sannan ta zaro sabowa dau ta mika mata tare da fadin ki rike kyauta sannan yau inasan kizo ki tayani kwana kinsan Abba yayi tafiya.
    Toh nagode ta fada tare da mikewa ta fice ranta fal farin ciki Amma tana mamakin yanda Auntyn ta koma haka.
    Rana fita ta sameshi yanata faman jiranta.
Hakuri ta fashi sannan ta mika masa kudinsa ta shige gida.

  Dan gajiya kam tagaji.
Toilet ta nufa tayi wanka tayi alwala sannan ta fito.sai da tayi shafa sannan ta shirya cikin Riga da skirt na atamfa sunyi mata kyau dan dinki ya zauna ajikinta gata tana da diri me kyau. Nan ta feshe jikinta da turare dan Aunty Naja na karo mata kayan cosmetic ba laifi duk karshan wata da inner wears.Har dinkuna tana musu ita da Shaheeda.tana gama shirinta tsaf ta yi sallah.
   Kitchen ta nufa ta dauki abincin ta dan tana samun abincin rana dana dare tunda ba dare ita takeyi.
    Zama tayi taci ta koshi sannan ta mike ta koma daki dan ta dan huta kafin kiran sallar magrib.



Bayan ta idar da sallah ishsha tana zaune ta tuna da cewar Aunty Rahma tace taje ta tayata kwana.
    Mikewa tayi ta sanya hijab dinta ta nufi part din nata.
    Lokacin data shiga babu kowa cikin falon dan  haka ta zauna saman kujera dan ta jira fitowarta.
    Abunka da gajiyayye bata dade da zamaba bacci ya dauketa.

  Wani saurayine ya fito daga cikin dakin Rahama na biye dashi abaya.
   Ganin Sapna cikin falon tadan tsorata amma da taga bacci take sai taji dan ddi.
    Kallan Sapna ya tsaya yi tare da fadin wannan fah?
    Ke da Allah muje mayi magana ta gidace ita.
   Amma gaskiya tayi amma zamuyi magana daga baya saida safe.
    Ta rakashi Har bakin kofa sannan ta dawo cikin falon tana kallan Sapna Har wani lashe lebe take kamar tsohuwar mayyah.
Ta kumayin murmushi ta shige dakinta.


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
 01 Amal fansclub 💅🏻🌷



Written by Zeenaseer😘
[17/1 22:18] Zeeenaseeer: 🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
       MARAICHI❣
               NA
  Zainab Naseer Sarki
      ( Zeenaseer😘)


2⃣3⃣

    💝💝
          Dis page goes to u BILKISU AMINU NURADDEEN.
     my god bless u my cwt hrt best wishes to u ix miji na gari🤗🤗
                            💝💝

⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
    Bata dau wani lokaci ba ta fito daga cikin dakin sanye da rigar bacci,wanda tsayinta ko gwiwa bai karasaba bata da maraba da raahinta.
Komai ana gani na jikinta.
    Cikin takunta na kasaita ta karaso wajan kujerar da Sapna ke kwance tana bacci hankalin ta kwance.
    Ahankali ta sunkuyo dai dai kuma tunta tare da sa harshe ta lasa.
   Da sauri ta firgita tare da mikewa zaune tana gyara hijab din jikinta.
    Murmushi Rahma tayi tareda zama kusa da ita ta sanya hannunta ta guda daya ta dago da fuskarta tare da fadin lafiya Sapna tashi muje ki kwanta.
     Janye hannunta tayi dafa jikin ta tare da fadin aa Niki barni anan zan kwana.
    Haba Sapna taya zan barki anan nikuma na kwana cikin daki ni daya.
Kenan kiranki bashi da amfani dan ki tayani kwana pls ki taso muje bacci nakeji.
    Ahankali ta mike tsaye tana gyara hijab din jikinta.
Itama mikewar tayi tare da shiga gaba Sapna na biye da ita a baya Har cikin dakinta.
    Gado ta nunama Sapna tare da fadin saiki cire hijab din ki kwanta ko kuwa.
   Tsaya tayi tana kallanta yayi da ita kuma Rahman ta zagaya dayan bangaran tana fadin saida safe.
    Bata tanka mataba illah hijab din data cire tana linkeshi harta gama ta ange kan wardrobe sannan ta kwanta tare da janyo blanket din ta kudundune,abunka da wanda ya gaji nan da nan bacci ya dauketa.
 
    Can cikin tare taji ana shafa ta.da sauri ta mike tare da saukowa daga gadan.
Ma kunnin fitala ta nema ta kunna.
 Da sauri ta juya baya tare da fadin innalillahi!
    Ba komai ne ya sanya taba fadin hakan face ganin Rahma kwance tsakiyar gado tsirarah.sai wani faman bankara kirji take.
    Ko karin bude kofa tashiga yi amma tankasa dan ta kulle dakin.
   Batareda ta jiwo ta kalle taba muryar ta na rawa tace Dan girman Allah Aunty ki budemin na fita.
    Ta sowa tayi Har gurin datake zaune ta sanya hannu tareda cire mata dan kwalin kanta.nan gashinta ya zubo Har gadan bayanta.
     Shafa mata kan ta shiga yi tareda shin shinata harta karaso kusa da kannan ta.
    Ita kuwa Sapna gaba daya jikintavrawa yake sabo da tsabar tsora da kuma mamakin abunda Aunty Rahman takeyi.
     Ahankali ta fara furta mata karkimin haka sapna pls ki taimaka min wallah nayi miki alkawarin kome kike bukata a rayuwar ki zan miki shi Mundin kika bani had in kai.
    Da sauri ta tureta ta fara ja da baya tana fadin wlh Aunty dana baki kaina na gwammace na mutu cikin wahala inda wata kan wannan ma a karo.
Cikin muryar kuka take magana.
    Ahankali ta durkusa Har kasa tareda hade hannayanta tana hawaye dan girman Allah Aunty kiyi min rai ki rabu dani na fita daga cikin dakin Ann dan Allah.
     Kara sowa wajanta tayi tare da hannu ta dago ta daga tsugunnan da take.
     Kiyi hakuri ba wani Abu zan miki ba kawai de ina San na sama miki gada kamar ko wace yr a duniyar nan me gata.ta karashe maganar tare da saka mata hannu cikin Riga tana kokarin shafa na fulaninta.
    Hankadata tayi tare da zagayawa ta shige cikin toilet da gudu tana kuka.
    Kulle kofar toilet din tayi da key taja da baya tana kuka.
     Da gudu ta karo wajan toilet din itama tana fadin wallah in baki budeba zan sa a karya kofar kuma ko kina so ko bakya so saina cika burina a kanki.


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
  01 Amal fansclub 💅🏻🌷




Written by Zeenaseer😘
[18/1 23:16] Zeeenaseeer: 🌳🌳       ⚜        🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
       MARAICHI❣
              NA
  Zainab Naseer Sarki
      ( Zeenaseer😘)


2⃣4⃣


   Da karfinta take buga kofar yayin da Sapna ke kara matsewa jikin bango tana hawaye.
 Baza ki bude ba wallahi zan sa a karya kofar.
Kawai ki yarda nayi miki alkawarin samun gata na Har abada.
 
  Cikin shasshekar kuka tace wallah da irin gata da zaki bani kwara na mutu da wahala inda wadda tafi wannan ina mataba da ita akan gatanki.
     Hmmmm yarinya kenan kina ganin kamar kin tsara ko?
   To wallah ki sabi zan nuna miki koni wace ce.

Kayanta ta sanya sannan ta fita daga cikin dakin.
   Sapna najin alamun an janyo dakin harda sanya masa key tayi.
  Da sauri ta fito daga cikin toilet din ahankali sannan ta zare key din ta kulle toilet din.
    Da gudunta ta karasa ta shige cikin wardrobe din dakin dama babba ce irin ta jikin wall din nan.
    Da sauri ta janyo kofar ta kulle tare da rufe kanta da kayan ciki duk da irin zafin data fara ji.


       Wayarta ta dauka tare da kiran wani yaranta akan yazo zaiyi mata wani aiki amma karya bari aga shigowarsa.
Sannan sukayi sallama dashi akan yana kan hanya.
    Tana nan zaune a falo tana Sara da marwa.
Lallai ma yarinya bakisan sharrinava yau zan nuna miki ni cikarkiyar yr bariki ce.
 
  Bayan kamar 1hr sai gashi ya shigo cikin gidan Dogo ne kakkaura yana da manyan gabobi gashi bakinkirin kana ganin sa kasan bashi da cikakken imani,idanun sa tamkar Jan gauta.
    Barka da zuwa dodo sunan da take kiransa dashi kenan.
    Yane! Yace da ita?
Allah sai de aiki me kyaune karki tasoni a banza.
   Hmmm! Kasan kaima ai bana kiranka dan karamin aiki.
Wannan babbanne toh zaka samu rabanka nima na samu nawa Amma fah sai kabi ahankali dan nan gidan sirikai nane.
    Ba komai me kike da bukata.
    Wata yarinya nake San ka daukomin tana cikin toilet kuma a cikin gidan nan.
   Na maka alkawarin kudi da kuma budurcinta.
   Dariya yayi tare da fadin Wallahi shine yafi komai sauki.
    Ywwa dama nasan baka da wasa shiyasa na nemo ka.
    Hakane muje ki nuna min inda take.
    Sannan ta nufi dakin yana binta a baya.


   Gaba daya ta gama jigata cikin kaya dan Har ta jike sharkab da gumi.
Dan tama nemi kukan ta rasa jira take kawai a bude ko fa ta gudu.
    Tana nan zaune taji karan bude kofa da sauri ta dauke numfashinta jin muryar namiji.



😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
 01 Amal fansclub 💅🏻🌷


Written by Zeenaseer😘
[19/1 21:42] Zeeenaseeer: 🌳🌳       ⚜        🌳🌳
🌳                              🌳
              👑👑
                🌳
     MARAICHI❣
             NA
  Zainab Naseer Sarki
      (Zeenaseer😘)


2⃣5⃣


    Har bakin kofar toilet din suka karasa.
   Yawwa tana ciki amma tasa key.
  Kallan kofar ya tsaya yi kafin yace amma kinsan irin wannan kofofin nada huyar sha'ani.
   Tou  yanxu meye abunyi.
   Baki da wani Abu da za'a iya sawa dole saide a kwance kofar.
   Amma kana tunanin hakan zai yiyu?
   Kawai inda hali koma ta yaya ne Akarya kofar nide kawai burina ta gane niba sa'ar yinta bace.
   Shiru yayi nadan wasu lokuta kafin yace inba damuwa zan iya zuwa na dawo.
    Eh zaka iya amma kayi sauri banasan asan da zuwanka cikin gidan nan.
    OK ba matsala yanzu zan dawo.

  Yana fita itama tabi bayansa sannan ta juyo ta dawo zuwa dakin.
Bakin gado ta zauna tana tunanin yanda zata bullowa al'amarin Sapna.

    Ita kuwa tana cikin wardrobe tagama jigata gaba daya duk jikinta yayi weak saboda bata samun enough iska.
    Gaba daya duk abunda suke fada akan kunan kunnan ta.
   Jin namiji ya fita tayi tunanin kode fitowa zatayi tana ganin inba namiji zata iya cin galava kan Aunty Rahman.
    Ahankali tadan tura kofar wardrobe din.
   Da sauri ta koma baya tareda tushe bakinta ganin Rahama zaune saman gado tana facing wardrobe din.
   Zuciyarta ce ta gaya mata kawai ta fita komai ta fanjama.
    Rufe idanunta tayi tare da fara salati cikin zuciyarta da neman samun nasara gurin Allah.
   Kawai bude kofar tayi ta fito da gudu ta nufi falo dan fita daga cikin part din.
 
    Rahma dake zaune bakin gado tayi saurin tsorata tare da mikewa ganin mutun ya fito daga cikin wardrobe dinta dan ita gani take Sapna na cikin toilet din.
    Bita tayi falon itama da sauri.
   Tsaye ta ganta bakin kofa tana ta faman kokarin bude kofar.
Da alama ta sakama kofar key.

   Hahhhahahah ta kama yin dariyar mugunta.
  Yaro besan wutaba saiya taka.
Ke Har kina tunanin kina da wani wayo ko?
 
  Jingina bayanta tayi tare da zameyawa kasa ajikin kofar tana hawaye.
   Da ker bakinta ya iya furta magana sabo da wani irin nauyi da taji yayi mata.
    Dan girman Allah Aunty ki rufamin asiri kamar yanda Allah ya rufa miki ki barni da irin kaddarar da nake da ita.
  Kada ki kuma saka rayuwata cikin wani duhun.
   Ki taimaka min ta karashe maganar tare da fashewa da wani irin kuka me tsuma zuciya.

    Sapna nike da burin haskaka miki rayuwa bana fatan kici gaba da rayuwa cikin kunci.
Wallahi nayi miki alkawarin kika bani hadinkai zaki dauwama cikin farin ciki dan tana maganar tana takowa zuwa inda Sapna take.

    Da sauri ta mike ganin tana yowa wajanta.
    Itama tafiya take da baya tana fadin wallah da kina kaunata bazaki taba gayamin irin wannan bah.
 Kuma wallah kika sake kika tabani saina kashe kaina.ta karashe maganar tare da rugawa zuwa cikin kitchen ta dauki wuka ta rike a hannunta.

       Kallan juna suka tsaya yi.
   Rahma ce ta kuma takowa.
   Dakata! Tace da ita kina kuma taku daya kuna kasheki kona kashe kaina.
Ta nuna mata wukar tana karkarwa dan gaba daya ta koma kamar mahaukaciya gashin kanta duk ya baje.na goshinta kuwa dana keyarta duk ya kwanta saboda gumin da tayi.

     Buga kofar aka shiga yi.
A lokaci daya suka juya dan kallan kofar sannan suka juyo suka kalli juna.
   Murmushi Aunty Rahama tayi tare dayin hanyar kofar dan budewa.
    Dube Dube Sapna ta shigayi dan samun abunda zata kare kanta dan tasan Mundin ta bude kofar nan kashinta ya bushe.
     Dinning ta nufa dan dauko wani katan flask me dauyi.

     Ita kuwa harta karaso wajan ta xura key din hannunta cikin kofar tana kokarin budewa.

    Da gudu ta karaso gun tare da buga mata shi a kanta.
    Batare da tayi wani kwakkwaran mutsiba ta badi kasa sumammiya.
      Yanda flask din hannunta tayi tana karkarwa ta kuma dannawa kofar key.
    Gaba daya ahankali ta ya tashi ga dodo sai faman buga kofa yakeyi.
    Ahankali tane ya dawo kan Rahma dake kwance a kasa ko motsi bata yi.
    Da sauri ta karaso wajanta tareda tsugunnawa ta kamo kanta tare da dorawa a kanta ciyarta.
   Jin lema a hannunta ta yasanyata saurin dubawa.
Jini ta gani duk ya bata gurin.
    Idanunta ta zaro tare da sanya hannun data shafo jikinta tushe bakinta.
Itama jinin duk ya bata mata kaya.
    Gaba daya hankalin ta ya gama tashi.
  Aunty!! Ta shiga kiran Sunanta tana jinjigata tana kuka.
 
     Da sauri ta mike daga kusa da ita tare da komawa gefe da baya da baya tana girgiza kanta.
     Durkushewa tayi tare da saka hannayanta cikin gashinta ta fashe da wani saban kuka.
 
 " Wayyo Allah na ni Sapna wannan wata iriyar mummunar kaddarace.yau nayi kisan kai kenan.koda yake gwarama a kasheni nima tunda rayuwata bata da wani amfani.
Tabbas ban cancanci zama cikin duniyar nan ba hausawa na fadin bayan huya sai ddi,amma ni gashi kullum abun kara gaba yake na shiga uku Allah na rukeka dan darajar wanda ka halicci duniyar nan dominsa Allah kadau raina a cikin daran nan dan bana fatan na wayi gari acikin wannan duniyar Allah".
  Fashewa ta kuma yi  wani saban kukan tana kallan Rahma a kwance.
     Idanunta ta kulle tare da furta kallamar innalillahi wa'inna ilaihir raji'un.
Ita taketa faman maimaitawa ko taji sanyi cikin zuciyarta😓

    Shikuma dodo daya gaji da bugawa kawai yyi tsaki tare da barin gidan dan bayasan wani ya gansa.


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
 01 Amal fansclub 💅🏻🌷



Written by Zeenaseer😘
[20/1 14:33] Zeeenaseeer: 🌳🌳       ⚜        🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                 🌳
       MARAICHI❣
              NA
  Zainab Naseer Sarki
      (Zeenaseer😘)


2⃣6⃣


Tana nan zaune kamar wanda nata dare dan ko motsi bata yi banda hawaye babu abunda ke zuba daga idanta guri daya take kallo amma ba komai take kallo ba gaba daya zuciyar ta shiga cikin rudani.
 
    Tana nan zaune aka fara kiraye kirayan sallar asbah.
   Maza tayi ta mike ta nufi toilet alwala ta dauro Sannan ta shiga yin sallah ba kakkautawa rana neman mafita wajan ubangiji.
    Tana zaune tana addu'a aka tada sallah.
 Mikewa itama tayi tareda tada sallar ta.
Bayan ta idar ne ta cigaba da mikawa Allah kukanta.

     Har gari ya fara aske Amma bata dena zubar da hawaye ba tana ta faman addu'a.

   Cikin ikon Allah ta fara motsa hannayanta.
   Hakan ya santa Sapna saurin mikewa dan duba halin da Rahman ke ciki.
 
   Ahankali ta mike zaune tareda dafe kanta idanunta a rumtse sabo da zafin da taji yana yimata kan nata.
 
    Da sauri ta matsa wajanta tare da fadin Sannu Aunty.

    Idanunta ta mike tare da saukesu kan Sapna gaba daya.
   Karfinta kuma zaro idan tana kallanta cikin mamaki.
   Zuciyarta ta fara tunanin abunda ya faru daran jiya.
  Ashefa yarinyar nan ce sana diyar ganinan cikin wannan halin zan koya miki hankaline ta fada cikin ranta sannan ta mike tana dafa bango.
    Da sauri ta matso dan taimaka mata.
   Daga mata hannu tayi alamun bata bukata.
   Jikinta a sanyaye taja baya ta tsaya tana kallanta Har ta shige cikin dakinta.
   Wata sassanyar Ajjiyar zuciya ta sauke tare da kuma yima Allah godiya daya sanya bata mace bah.
 
    Ruwa ta dauko da da abun duster dan goge gurin datasan ya bace.
Saida dakin yayi tas sai kanshi freshener yake sannan ta bude dakin tare da fita.
     Da sauri ta nufi part dinsu.dan lokaci ya kuri sosai.
   Ganin Safiya bata cikin dakin ya sanyata kaduwa dan mamaki ta tafi makaranta.
Yanzu kenan meye abunyi dan bata San zaman gidan kwata kwara baya mata ddi.
    Jikinta a Sanyaye ta nufi toilet dan yin wanka.
   Dama ita makeup be dame taba,doguwar Riga ta sanya ta dan shafa farar powder a fuskarta ta gyara gashinta sannan ta dure kanta da dankwali.
    Ji tayi wata kasala ta saukar mata sakamakwan baccin da batayi jiyaba.
   Matsawa tayi kan gadan tare da lumshe idanunta nan dannan bacci ya dauketa.


Tana shiga daki toilet ta nufa tayi wanka sannan ta fito ta janza kaya ta dauki magani tasha dan Ciwan da kanta yake mata.
     Itama gadan ta koma dan hutawa.
    Hmmm! Ni Rahama wata zatayi kokarin kashewa lallai yarinya baki da hankalin zan nunana miki baki da gata a fadin duniyar na. Kuma yanzu kika fara shiga cikin tsanani.
     Da wannan tunanin itama baccin ya dauketa.


Sai kusan karfe biyu Sannan Sapna ta farka daga baccin da take yi.
  Ahankali ta sauka daga kan gadan ganin 2:43pm gashi ko sallah batayiba ga yinwa datake faman ji.
     Toilet ta nufa ta dauro alwala sannan tayi sallah tasan Safiya ta dawo daga makaranta dan ganin yanda ta watsar da kayan ta a kasa dama haka takeyi koda yaushe kwata kwatanta kazamace babu abunda ta iya.
    Sai da ta gyara cikin dakin sannan ta nufi kitchen dan dauko abincin ta dan wata iriyar yinwa da take ji.
      Cikin sa'a kuwa an gama abinci ta dauko kenan ta fito daga kicin din sukaci karo da safiya abinci ya bare a kasa gaba daya.
     Da sauri safiya taja da baya tare da dura wata uwar Ashariya.
    Ita kuwa durkusawa tayi dan kwashe wanda beshafi kasa ba.
      Kafa tasa tare da take abincin tana fadin dan uwarki kin matamin kayana da abinci amma sabo da baki da hankali baza ki ma duba niba saide ki tsaya kina wani kwashe abinci sai kace mayyah.



😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
  01 Amal fansclub 💅🏻🌷


Written by Zeenaseer😘
[20/1 20:34] Zeeenaseeer: 🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
        MARAICHI❣
                NA
 Zainab Naseer Sarki
     ( Zeenaseer😘)


2⃣7⃣


   Mikewa tayi tsaye tare da kwada mata mari sannan cikin kuka tace uwarki kike zagi.
    Kuma kace mayyah mahaukaciya wanda batasan darajar abinciba.
   Kebar ganin ke yaya tace wallah kawai sabo da Umma nake raga miki.mutun marar baki shine dan iskako?

    Hannun ta rike da fuskar ta cikin mamaki ta nuna kanta tare da fadin ni kika mara Sapna?

    An mareki kuma kinsan ba karfina kikafi bah.
   Nan itama takai hannu zata rama suka hau dambe dama Sapna tafi Safiya karfi.
   Safiya najin wahala ta dauki murfin tukun ya ta kwalama Sapna a kanta nan ta fasa mata goshi ya fara jini.
   Da sauri ta saketa taja da baya tare da dafe gurin ganin jini na zuba tace ni kaka fasama kai.
   Kukan kura itama tayi tare da turata ta buga kanta itama da abun sick na kitchen din.
 Nan take kanta itama ya fashe.
 
   Jin zafi kuma ga jini na zuba ya sanya ta bude baki ta zunduma uban ihu.
  Wanda yasanya Umma da hafsa fitowa daga daki da gudu jin ihun safiya.

   Kitchen din suka nufo.da sauri suka karasa wajan Safiya dake kwance a kasa jini na zuba a kanta.
 
    Umma ce tace laaah!
Shikenan ta fasa mata kai zata kashe ta.
   Hafsa ce ta shaki huyan Sapna cikin daga murya ta fara fadin.
   Ubanme ta miki kika fasa mata kai.
   Cikin kuka tace ni bakuga yanda ta fasa min kainaba kodanni bani da gata.
    Taasssa! Ta kuma kasheta da mari tare da fadin ni kike gayawa wannan maganar shegiya mayyah.
   Cikin kuka tace wallah niba mayyah bace akanme zata fasamin kaina,in bani dame ramamin a duniya a lahira Allah zai yimin sakayya.
     Yimin shiru munafuka,Umma ta fada tare da taso zuwa wajan da Sapna take tsaye ta hau dukanta tana masifa kamar Allah ya aiko ta.
    Da ker ta rabu da ita ta koma gefe tana huci sannan tace bade akan abinci ake fadanba toh wallah sai bayan kwana biyu zakici abinci a gidan nan.
    Sannan ta koma ta kama safiya sukabar kitchen din itama hafsar tabi bayanta suna zagin Sapna dake kwance a kasa cikin wani irin mahuyacin hali na rai ko mutuwa.

    Banda kanta dake jini yanzu harda baki da hanci dan buskarta duk ta kumbura dan ko daga hannunta bata iyawa sabo da jikinta yayi tsami.
   Har gefan idanta saida ya kumbura hawaye ne ke zuba ta gefe da gefen idanta.
   Tana nan a kwance tana numfashi sama sama sabo da ta daku.

    Ahankali tafara motsa yn yatsun hannun ta dana kafarta.
   Karfinta dafa hannun a hankali ta mike zaune tana cige lebanta na kasa.
Da ker ta kama window ta mike zaune.
   Haka ta fito daga cikin kitchen din tana dafe dafe ahankali harta samu ta fito waje dan bamata gani sosai dishi dishi take ganin garin.
    Tana tako kafarta waje ta kuma faduwa kasa.
   Ooch! Ta kuma fada tana kwance a kasa kuma fashewa tayi da kuka maras sauti dan ita kadai tasan yanda take ji.{ni kaina tafan tausayi Har kullah na zubar mata😓}

     Ji tayi baza iya tashiba lokacin.haka ta yini kwance a tsakar gidan nan ba me tausayinta.
    Har bayan sallah magrib tana kwance koda suka fito suka ganta babu me karfin imani a cikin au haka suke harkokinsu ko kallanta basamayi.
    Saida taga gari ya fara duhu.ta lallaba ahankali. Dan ta shiga cikin daki.

Hafsa ce ta fito zata tafi gida su Umma suka rakota Amma suna ganin yanda take Jan jiki tana kokarin shiga daki haka suka huce ta ko tausayi babu.
    Safiya kuwa ji tayi babu ddi dan tabata mugun tausayi Amma itama haka ta huce ta barta anan.

    Ahaka taja jiki Har cikin dakin sannan ta kwanta a tsakar dakin tana maida numfashi.
    Haka ta daure ta mike ta nufi toilet.
 Tana kuka tana gasa jikinta harta fara jin ddi.
Fuskarta duk tayi wani irin dan dukan da tasha.
   Saida taji ta gasa ko ina bataji Ciwan sosai sannan ta fito daga toilet din ta sanya Riga da wandanta masu taushi..
    Azaunema ta iya yin sallah dan yanda take jinta.
   Kofi ta dauka ta nufi toilet ta dauko ruwan zafi sannan ta dauki Lipton ta sanya shiga tasha tea din ta gasa cikinta.
    Da ker ta nemo wani paracetamol tasha ko zataji dadin jikinta.
Bayan ta gama sha nan kan abun sallah ta zauna tana tunanin wata badakalar dazata fuskanta wajan Rahama da ya Abba. Shin menene mafita arayuwata kode guduwa zatayi daga gidan.
   Toh amma inta gudu ina zataje wata sani kuma wajanwa zata.wannan tambayoyinne zuciyarta ta kasa bata Amsarsu.
   Idanta ta rumtse tana sauraran kiran kiran sallar ishsha da akeyi.
   Ahankali ta gyara zamanta ta tayar da sallah bayan ta idar saida ta dau lokaci tana kuma kai kukanta ga ubangiji sannan ta kwanta kan abin sallah bacci ya dauketa.

  Bata jima da kwanciyaba safiya ta shigo cikin dakin duk sai taji ba ddi ganin yanda Sapna ta koma ta dalilin su.
   Tayi fari so sai ta rame gashi kuma duk fuskarta ta kumbura saboda dukan da Umma ta mata.
    Dakinta Shiga ta dauko blanket ta rufeta sannan ta kashe mata wutar dakin ta shige itama ta kwanta.



😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
  01 Amal fansclub 💅🏻🌷



Written by Zeenaseer😘
[21/1 11:43] Zeeenaseeer: 🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
       MARAICHI❣
               NA
 Zainab Naseer Sarki
     ( Zeenaseer😘)



2⃣8⃣


    Can cikin dare ta farka saboda wata iriyar yinwa da take damunta.
   Ahankali ta mike ta nufi kitchen din dan samun abunda zataci duk da a tsorace take dan tana ganin kamar Umma zata kamata.

    Tana tura kofar ta kunna wutar kitchen tahau bude budan kwanika amma bbu alamun abinci ko dugo.
    Da sauri ta juya gurin wanke wanke tana neme neme.cikin sa'a ta bude wani flask tuwone gaya babu miya.
   Zama tayi tanata ci kamar wanda ta shekara bataci abincinba.saida taji cikinta ya fara tasowa sannan ta mike ta dauki ruwa tasha sannan tayi gyatsa.
   Taji ddin ganin tuwannan sosai duk da gaya ta cishi.

  Daki ta shigo tare da turawa ta kulle.
  Kan abun sallar taga blanket da mamaki ta tsaya tana kallo dan itade tasan bata dau koba amma ya akayi hakan dan tasan ko sanyi zai kasheta Sapna bazata rufeta ba.
   Kafada ta daga tare da fadin maybe ma nina dauko ban saniba.
    Saman kujera ta hau tare da lullube wa nan danan ta koma baccin da tana bukatar hutun.


Saturday [ 6:32am ]🌝
     Lokacin ta farka daga bacci dan ta makara sosai ita da tasaba tashin asbah.
   Toilet ta nufa ta dauro alwala sannan ta tada sallah bayan ta idar tana zaune saman abun sallah tana en addu'o'in ta da tasabayi ko wace safiya.
   Tana idarwa ta shafa sannan ta nade sallayar ta maida ma ajjinta.
 
    Har yanzu fuskar ta bata saceba daga kum burin da tayi ga saman goshinta inda ya fashe shima yayi kullutu.
     Kitchen ta nufa ta hadu katan wanke wanke takai inda akeyi sannan ta gyara kitchen din.
    Ruwan tea ta dura sannan ta fere doya ta Dora.
   Bayan ta juye ruwan tea din sannan ta gyara kayan miya tayi musu yr stew.ta soya doyar da kwan ta anje.
     Tana gamawa ta kuma wajan wanke wanke ta shiga yi Har ta gama.
   Bayan ta gama jere kwanikan a kitchen ta dauki tsintsiya ta share tsakar gidan.
   Duk wani aiki da tasan nata ne tayi ta gama.

   Dakin ummane kawai bata bare ta gyara mata ita kuwa hakan ba karamin dadi yayi mata bah.

   Dakinsu ta nufa ta gyara shi duk safiya nata faman bacci dan ko sallah batayi sai lokacin da ta tashi tukun ko karfe nawane.
    Toilet ta wanke sannan tayi wankanta ta shirya tsaf dan tau tana cikin farin ciki shiyasa tayi aikinta da huri.
   Dan duk karshan wata ana kawo Shaheeda ta yini yau kuma gashi assabar kuma za'a kawo ta.
Shiya take kokarin kore duk wata damuwa dake cikin ranta dan batasan yr uwar tata ta gane tana cikin wani hali.

    Sai kusan 10am sannan ta gama duk abunda ya kamata.zuwa tayi ta mike kan kujera tare da kallan saman rufin dakin tana tunanin rayuwa.
   Tana nan kwance batasanma lokacin da Safiya ta tashiba.
   Wanka tayi itama ta tsara kwalliyarta.sannan ta sanya kaya ta fita daga cikin dakin.
    Karan rufe kofa ne ya sanyata dawowa daga duniyar tunanin da tatafi.
   Zaune ta mike tare da kallan agogon dakin da ganin 11saura Amma Shaheeda bata zoba.

     Bata gama tunanin ba taji sallamar ta da sauri ta mike tare da rungume ta itama rungume tan tayi sabo da murnar ganin yar uwar tata.
    Janyota tayi tayi suka zauna kan kujera ta shiga kallanta tana sha'awar yanda ta kara girma.da yake Ita rana da girman jiki tayi fari tayi kiba tayi mulmul da ita ga kwalliya kayanta kala kala gwanin ban sha'awa.
 
    Ya Sapna ya gidan da kowa da kowa.
   Murmushi tayi tare da shafa fuskar tace lafiya qlau yr lukuta.
       Dariya ta danyi tare da fadin kai yaya nice yar lukutar.
    Eh mana kinaga yanda kika koma kuwa ai kinyi biyuna.
    Dariya ta kuma yi sannan tace ya dan Asabe yana gaidake.
   Duk da tasan karya take kawai ta fadane dan taji ddi.
    Kanta a kasa tace ina amsawa.
    Kai! Ya Sapna meya sameke duk fuskar ki tayi wani iri.
     Shiru tayi bata bata amsaba saida ta kuma maimaita mata tambayar sannan tace bigewa nayi.
Ta shiga lalubar ledar data shigo da ita tana fadin me kika kawomin yar kirki.
    Itama bata yarda da abinda sapnar ta fada bah saita danne ledar alamun bazata badaba.
    Dago da idanta tayi ta kalleta da mamakin hanata daukar ledar sannan tace ki gayamin ya Sapna meya sameki.
     Ohh! Shaheeda dole sai kinji believe me mana na gaya miki abunda ya faru aa ya kikeso nayi ne.
    Am sowie sis I don't means to upset u Jst am caring ne Amma shikenan. Kinga ta shiga dauko mata abubuwan cikin ledar tana murmushi tana nuna mata.
Kinga wannan duk abunda yaya ya siyamin nake tara miki
Chocolate, biscuit da sauran su.
    Kallan ta kawai Sapna keyi duk da karancin shekarunta tana da hankali.
    Kin gani ya Sapna taci gaba da nuna mata duk dan ta sanyata farin ciki.
    Sannan ta kuma janyo wata ledar tace kinga duk juice ne nake tara miki nasan kina so ko.
   Totally speechless dan batama da bakin magana sai ido take zuba mata.
    Ya sapna kinga kudin makarnta na 50 saina raba biyu na anje miki rabi tunda nasan kinaso ko?
    Batasan lokacin data rungume taba tana kuka.
   Shiru tayi rike da kudin a hannunta tana jin sautin kukan yayar tata.
    Sapna duk wannan abun niya kamata ace ina miki amma bani da damar hakan.
     Ahankali ta janye jikinta daga nata itama hawayan take tasa hannu tana goge mata tare da murmushi tana girgiza kai alamun ta daina kukan.
     U deserved it sis,ur my world,everything mind is belongs to u even my self.even god knows hw I feel about u dats y,am still here for u I rwwly Lov u nd I always Will♥
      Kuma rungume ta tayi tana kuka sannan ta danka mata kudin a hannunta ta tana murmushi.
      Sapna! Sapna!! Taji murya Ya Abba na kwala mata kira.
   Gabantane yayi mugun faduwa take suka kama kallan juna ita da Shaheeda,
Hannu ta Dora aka tare da fadin nashiga uku 🙆🏻



😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
  01 Amal fansclub 💅🏻🌷



Written by Zeenaseer😘
[21/1 22:34] Zeeenaseeer: 🌳🌳       ⚜        🌳🌳
🌳                              🌳
              👑👑
                 🌳
      MARAICHI❣
             NA
 Zainab Naseer Sarki
     ( Zeenaseer😘)


2⃣9⃣


•••••• kallanta Shaheeda keyi da mamaki tare da fadin ya lafiya menene.
    Tsaye ta mike tana yarfe hannu tana durawa akai ta kasa tsayawa waje daya.
   Haba yaya wai meye duk kabi kika wani rude kamar wanda tayi kisan kai.
   Gaba daya ta kasa magana sai da ya kuma kwalla mata wani kiran sannan ta fice da sauri batare da tabi takan Shaheeda dake tsaye tana tmbayartaba.
    Da gudu itama ta bita suka fice tsakar gidan.
   
    Tsaye yake a tsakar gidan yana jiran fitowar ta daga cikin dakin yadaure fuska babu alamun murmushi atare dashi.
    Matsawa tayi gurinsa tare da durkusa jikinta na rawa murya na karkarwa tace yaya gani.
    Ita kuwa Shaheeda tana tsaye kofar daki tana mamakin yanda duk Sapna ta wani rude kan ya Abban babba da ita.
Ai gani take ko kita karama bazata rinka rawar jiki akan saba.
Tsaki taja dan tsabar jin haushin ta.

   Tun dazo me kikeyine kinaji ina kiranki kika yimin shiru.
    Am..m..um. Ba shiru nayiba na amsa bakaji bane.
   Toh kije ki yima Rahma duk abunda ya dace bata da lafiya ne.
   Toh ta fada da sauri.
 Kanta a kasa.
    Harya juya zai tafi ya hango Shaheeda tsaye bakin kofa tana kallansa cike da jin haushi da tsanarsa.
 Cikin tsawa yace ke baki iya gaida mutane bane.
    Kallansa tayi tare da zunbura baki alamun shagwaba sannan ta shige dakin ta kulle.
    Tsaki yayi ya fice dan zata iya bata masa lokaci.

   Mikewa tayi sannan ta fara knocking dakin dan Shaheeda ta bude.
   Ahankali ta mike daga kan kujera ta bude mata dakin.
   Tana shigowa itama ta zauna tare da sauke wata Ajjiyar zuciya sannan ta kalli Shaheeda da murmushi kafin tace bara naje na dawo yr kanwata.
    Tashi tayi tare da fadin aa wallah yaya saikin ci abunda na kawo miki maybe ma baki karyaba.
    Murmushi tayi tare da fadin you boss.
   Dukansu suka yi dariya.
Saida taci biscuit da juice din harta koshi sannan tace zan iya tafiya.
    Itama mikewa tayi tare da fadin mutafi tare saina tayaki aikin.

Tare suka fito daga cikin dakin sannan suka nufi part din Abban suna tafe suna hira Har suka karasa.
   Da sallama suka shiga cikin falon,ganin ba kowa ya sanyasu shigewa.zama shaheeda tayi kan kujera tana karewa dakin kallo ba laifi dakin yayi kyau ta fada a zuciyarta.
     Kitchen ta nufa ta fara gyarawa sannan ta dura abinci.
    Suna hira da dariyar su tana aikin itama tana tayata da wani abun Har ta kammala komai.
   Tunda suka shigo cikin gidan Rahma bata fito ba hakan ya ba Sapna damar sakin jikinta tayi aikinta a nutse harta gama.
     Saida suna gaf da gamawa sannan ta leko daga cikin dakin tace da Sapna ta kawo mata abinci.
    Zubawa tayi ta hada komai sannan ta bawa Shaheeda ta kai mata.
   Ansa tayi ta nufi dakin,da sallama ta shiga cikin dakin.
   Tana zaune a gaban mirror tana kwalliya.
  Anje mata abincin tayi tare da nufar kofa zata fita.
   Tunda ta shigo take kallanta ta mudubin yarinyar ta burgeta sosai duk da ba wata babba bace.
     Ke kuma daga ina haka zaki shigoma mutane daki babu sallam balle ki gaida mutun.
    Ya Sapna ce ta aikoni in kawo abinci koma na kawo.tana kaiwa nan ta fice daga cikin dakin.
    Cike da mamakin maganganun yarinyar ta juyo tana kallan kofar tana tunanin duk inda yarinyar nan ta fito kanwar Sapna ce dan suna kama amma Sapna ta dan fita kyau.
     Murmushi tayi tare da juyawa taci gaba da abunda take tana fadin kaya sun karu.

  Suna gama abunda ya kawosu bayan Sapna ta zuba musu abincin sunci sun koshi sannan suka fito daga part din.
   Suna kokarin shiga part dinsu sukaga Safiya taci uwar kwalliya zata fita.
    Ko kallanta Shaheeda batayiba.
   Har sun kusa hucewa Sapna tace Shaheeda baki gaida ya Safiya bah.
    Dan Allah yaya kitaho mu tafi itama ai bata mana maganaba.
    Ita kuwa Safiya tana jinsu tayi fice warta.
     Shigewar gida itama tayi Sapna ta bita a baya tana mamakin hali irin na Shaheeda tun tana karamarta ga shegiyar zuciya.
     Cikin daki ta sameta zaune.
   Shaheeda meyasa kika raina mutane ne.inaga tunda kikazo gidan nan ko Umma bakije kin gaidaba.
    Nifa yaya duk wanda baya sanki nima bana sanshi kuma duk in gidan nan basa sanki.
     Waya gaya miki kowa yana sona kawai de kinasan ace baki da kunya yanzu ki tashi muje ki gaida Umma.
    Nifa gaskiya ya bana santa kuma bazan gaida taba ta karashe maganar da kuka.
     Rungume ta tayi tare da fadin ya isa haka pls Amma ki dena rashin kunya kinji.
    Kai ta daga mata tare da fadin kema yaya ki daina kula su kinji toh ta fada.
      Yanzu muyi sallah saina rakaki ki gaida Aunty Naja ko?


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
 01 Amal fansclub 💅🏻🌷



Written by Zeenaseer😘
[22/1 22:58] Zeeenaseeer: 🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                 🌳
      MARAICHI❣
            NA
 Zainab Naseer Sarki
     (Zeenaseer😘)


3⃣0⃣
   
         Dis page goes to 💋💋Precious writer✍🏻
  Ubngiji Allah ba barmu tare ya kara basira da kuma kwarin ido ya kuma karemu daga Sharrin makiya da mahassada.
     Ya kuma daukakamu ya bamu abunda muke nema ya cika mana burikanmu na alkhair😍😍😍
 


         Bayan sun idar da sallah ta gyara fuskarta suka fita itada sapna suna hira gwanin ban sha'awa sai labarin makarantar su take bama sapna tana dariya Har suka karasa gidan.
    Da gudu Shaheeda ta shiga tare da rungume Najar tana murnar ganinta.
    Sapna murmushi kawai takeyi tana kallan yanda kanwar tata kema Aunty Najar shagwaba ita kuma tana biye mata.
    Zama tayi kan kujera tare da fadin Aunty ina yini.
   Lafiya qlau Sapna ya karatu da kuma en gidan.
   Kowa lafiya Aunty.
 Toh masha Allah.
     Aunty kince innayi kokari zaki shiya min waya ko.
   Eh hakafa nace yr kirki.
   Toh mun kusa fara jarabawa zanyi kokari dan asiyamin waya.
   Sapna dake zaune tace ke kuma me zakiyi da waya.
   Kaiii! Ya Sapna kefa zan bawa.dan nima a makarnta in ana labari ince nima sis ina tana da waya.
   Dariya sukayi dukansu dan tabasu dariya barin yanayin yanda tayi maganar.
    Lallai wata yarinya nasan yayarta da yawa.Aunty Naja ta fada.
   Hira suka tayi wani lkcn Sapna na sako baki wani lkcn ko saide tayi dariya.
    Har kusan magrib sannan aka aiko ana kiran Shaheeda da yake in tazo dan Asaban cewa yake ta tafi gidan Naja saiyaje can ya dauketa.
    Nan ta mike ta fara saka takalminta.
  Har waje Sapna ta rakota dan zata tafi gida Har tayima Naja sallama.
    Yana cikin mota a zaune.
   Hannun ta rike dana Shaheeda ta karaso wajan duk da tasan ba wani kulata zaiyi bah.
    Har kusa da side dinsa tazo yayin da ita kuma Shaheeda ta zagaya dan shiga.
 
    Kamar zatayi kuka tace yaya ina yini.ko kallan idan take beyiba ya ja motar yabar gurin.
Tana kallan motar Har ta bar lafin wata kwallace ta kuma cuko idanta.
   Ahankali ta sanya hannunta ta goge tare da bin hanyar tafiya gida cikin nutsuwa.
   Ahankali motar sa tayi parking agabanta.
Fitowa yayi sanye yake cikin blueback jeans da White shirt.sai bakin space a idansa.
 Kyakyawa ne Dogo amma baza a kirashi da baki ba irin chocolate colour din nanne gashi ya hada da Hutu shiyasa aina yin colour dinsa ya fito.
Guy din ya hadu sosai.
     Cikin takunsa na kasaita ya karo Har inda ita ke yatsa.
   Itama tunda ya fito take binshi da ido dan ya burgeta.
   Cikin sanyin murya ya furta yn mata sannufa.
   Batareda ta kula shiba ta fara neman hanyar hucewa.
    Gabanta ya shiga tare da zare glass din idanunsa.
    Ya kuma zaki tafi bakiji meke tafe dani bah.
    Ahankali ta furta kayi hakuri ina saurine magrib ta kusa kuma za'a iya yimin fada a gida.
   Toh shikenan naji ki yimin kwatancan gidan naku.
   Da Sauri ta dago kai ta kalleshi.
    Shima itan yake kallo gira ya daga mata alamun eh!
   Kanta ta sauke da sauri tare da fadin hakanma bazai yiyu ba pls ka barni na tafi ina tsoran karnayi dare.
    Ohk! Naji hannun sa ya sanya cikin aljihun sa tare da fito da wata yr madedeciyar waya kirar iPhone5 ya mika mata tare da fadin gashinan pls in kin koma gidan ina San yin magana dake.
    Kallan sa ta tsaya yi tare da fadin waya cefa ka bani.
   Eh fah nasani ai dan Allah ki karba mana.
     Kanta ta shiga girgiza tare da fadin gaskiya ka rike kayanka kayi hakuri na gode amma bazan iya amsaba.
    Nikuma saikin amsa ko kuma duk inda kikayi saina biki.
     Dan Allah ka rufamin asiri wlh inna amsa fada za'a yimin a gida.
    Babu wanda zai miki fada amma in baki amsa bane za'a miki fadan.
    Jikinta na dar dar ta amsa tare da hucewa gaba.
   Murya yadan daga tare da fadin ba sallama.
    Ita kuwa ganin lokacin da wowar Abba ya kusa ya sanya take sauri gashi yana neman bata mata lokaci.shiyasa ta amshi wayar.

    Da sallama ta shiga cikin gidan fanin bai dawoba ya sanyata jin ddi.
   Alwala tayi dan gabatar da sallah magrib. Bayan ta idarne tana zaune tana addu'a taji karan waya.harta dan tsorata sai kuma ta tuna da wayar dazu.
    Mikewa tayi tare da kulle dakin dan kar Safiya ta ganta tana waya.
    Bata sha wahalaba dan gane yanda ake daga kiraba dan irin wayar Husnah ce komai da komai kuma tana ganin yanda ake amfani da ita.
      Da sallama ta kara a kunnan ta.
  Shima amsa mata sallamar yayi.
Sannan yace da fatan ina waya da sapna.
    Eh ta amsa tare da fadin amma ya akai kasan sunana.
    Murmushi ya danyi kafin yace bakiji hausawa na fadin Mesan abunka ya fika dabara bah.
    Uhmmm! Kawai ta iya cewa.
    Wato sapna a gaskiya na jima ina kaunarki amma Allah yayi sai yau muka hadu.tun ranar dana fara ganin ki na rinka bibiyarki harna gano ko ke wacece.
       Nide sunana Kamal kuma kuma iyayena haifaffun yn garin nanne amma muna zaune a Kaduna yanxu hakama naxo gidan kakanninane.
     Shiru tayi tanata faman sauraransa.
    Yanaji kinyi shiru bakice komaiba.
    Murmushi tayi tare da fadin toh me kakeso nace.
   So nake ki bani amsar bayata insan amatsayin da nake ciki.
    Kayi hakuri gaskiya kadan bani kona biyu.
   Shikenan insha Allah, nagode I Lov u sannan ya kashe wayar.
    Tsayawa tayi tana kallan wayar kamar karya dena magana.
    Murmushi takumayi tabbas babu macan da zataga Kamal bata kyasaba.
Amma ita ya zatayi yanzu itada ko sakewa batayi a gida bare a ganta tana hira da wani.
    Zuciyar tace ta bata shawarar kawai ta rabu da shi ta hutama kanta.
    Kashe wayar tayi gaba daya tare da zuwa ta boyeta cikin kayanta.
 

       Shi kuwa kamal yana gama waya da Sapna ya nufi fridge din  dakin tare da dauko katuwar kwalvar giya.ya bude ya kafa kai yasha ya koshi sannan yayi gyatsa.
    Sannan yayi murmushi tare da fadin burina ya kusan cika.
    Da wata mahaukaciyar dariya ya kuma kyalkyalawa sannan ya mike tare da daukar sauran kwalbar ya fita daga dakin yana sha yana maganganu shi kadai.



😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
  01 Amal fansclub 💅🏻🌷



Written by Zeenaseer😘
[23/1 21:25] Zeeenaseeer: © Exquisite Online Writers✍🏻


🌳🌳       ⚜       🌳🌳
🌳                             🌳
              👑👑
                 🌳
      MARAICHI❣
              NA
 Zainab Naseer Sarki
     (Zeenaseer😘)



3⃣1⃣


   Koda dare yayi gaba daya ta kasa bacci babu abunda take gani sai Kamal da zarar da rufe idanunta.
   Haka ta rinka mutsu mutsu dan babu wani Abu me kama da bacci acikin idanunta.
    Ahankali ta mike ta nufi inda ta ajje wayar ta Dauko ta takunna dan gani take kamar zai kara kiranta.
   Haka ta sama wayar ido tanata kallanta.
Tana nan zaune da wayar a hannunta bacci ya dauketa.

  Kiran sallah da akeyine ya tasheta daga baccin da take.
  Afirgije ta mike ganin inda take kwance tana dubawa kasa taga wayar da take hannun tace harta fado kasa bata ganiba.
    Cikin wardrobe dinta ta maida ta anje sannan ta yo alwala dan gabatar da sallah asbah.
   Tana idarwa ta koma dan baccin be ishetaba.



    Lokacin data farka Har rana ta fito dan 8am tayi.
   Kitchen ta nufa ta fara aikin daya kamata tayi tayi girki sannan tayi wanke wanke da gyaran gidan.
   Kowa yana daki yana bacci sai ita kadai kamar baiwa a tsakar gidan tana aikinta tana tuna Kamal sai taji gaba daya ranar tana cikin farin ciki.
      Bayan ta gama aikinta.ta shigo daki tana nishi kan kujera ta zauna dan tana bukatar hutawa.
     Mikewa tayibta gyara dakin nasu sannan tayi musu wankin bandaki.
   Wankanta tayi ta sanya kayanta tayi kyau da ita.
    Dakin Umma ta nufa dan tana jin yinwa sosai.
    Ta dauki plate da kayan Karin ta kaimata.
    Tana zaune kan kujera a falo ta shiga da sallama. Sannan ta gaidata.
    Bayan sun ta agnje abincinne tace Umma ga kwano na nan inajin yinwa.
 
    Mikewa zaune tayi batare da ta tanka mataba ta bude flask din ta dibi abinci ta zuba mata wanda ko dan yaro yayayye akama maybe yayi masa kadan.
    Daukar plate din tayi tana kallan abincin da mamaki duk da ta saba zuba mata kadan din.

    Menene kika tsaya kina kallona ko abinci yayi miki kadan jaka uwar ci.
 
   Girgiza kanta tayi alamun aa,sanna ta fita daga dakin.
    Kitchen ta nufa ta zauna tare da yin Bismillah sannan ta sanya abincin cikin bakin,cikin ikon Allah tana gamawa tasha ruwa sai taji abinci ya isheta ta goshi.
   Plate din ta wanke sannan ta mai dashi inda yake.
   Lokacin da zata shiga dakine taci karo da Safiya tana kokarin fitowa daga dakin itama.
    Babu wanda yayima wani magana IRA tana fita ita kuma ta shige.
   Da sauri ta karasa wajan data ajje wayarta.
   Tana zuwa kuwa aka kira.da sauri ta daga dan murna.
    Sallama tayi masa.
Shima cikin muryarsa me sanyi ya amsa mata sallamar tata.
     Bayan sun gama gisawane yace toh sapna da fatan zan samu kyakyawa saka mako ko?
   Murmushi tayi tare da fadin insha Allah kuma na amince ka zama abokin rayuwata.
   Toh kinga Alhmdullh nagode sosai Allah ya barmu tare amma ya kikesan muyi kenan kince gidanku ba'a barin ku tsaya da samari.
   Hakane amma karka samu damuwa in ka samu lkc sai ka zo inda muka hadu muna gaisa.
    Yawwa my one nd only na gode sosai Allah kuma ya bani ke amatsayin uwar yayana.
    Wani sanyi taji cikin zuciyarta tare da fadin amin.
    Yanzu ina da wani dan abunda zanyine amma kibari anjima zamuyi waya.
    Toh tace dashi sannan sukayi sallama.
    Murmushi ta kumayi tareda rungume wayar a kirjinta ta kuma rufe idanta.
    Gaskiya taji ddi sosai da Allah ya bata mai santa kamar Kamal.
Gashi lokaci daya wani irin sanshi ya shiga cikin zuciyarta.

  Shikuwa suna gama wayar ya kalli abokinsa dake zaune kusa dashi tareda tafawa.
    Bashir da suke kira Bash ya kuma kwashe da dariya tare da fadin wallah ta kamu.
     Murmushi Kamal yayi tare da fadin an gaya maka nina wasane kadan ma ka gani.
    Hhhhhhh! Allah ko mutumina.
 Sosaima kuwa kaima in banda abunka me zanyi da wannna kucakar yarinyar da kanta yake cikin duhu ai nafisan wa yaryiya sai tafi kawo light amma wannan guy ina zani da ita.
    Dariya bash ya kuma yi tare da fadin baka da wasa mutumin.
    Kaide bari ai so nake wannan Karin na bawa Leon mamaki wallahi wancan karan naga sai wani ririta Jameel yake.


KAMAL💀
    Yarone meji da kudi da kasaita ga kyau inkaganshi sai kayi tsammanin dan gidan gov.ko shugaban kasa.
Asalinsa wani dan taxine ya tsinceshi ya ringa cigiyarshi karashe sai gidan marayu ya kaishi.
    Haka ya taso cikin yn uwansa.
Yarone me kiriniya da rashin ji gashivtun yana karami ya iya mugunta kullum saiya jima wani rauni cikin gidan nan.
Har zuwa lokacin daya girma.
   Yayi karatunsa na primary Har sakandire Har zuwa jami'a saboda yaran yana da kokari.
   Lokacin da zaiyi degree dinsa na biyu gov.ta zabi masu kokari acikinsu harda shi suka sami scholarship zuwa China karatu.
   Bayan ya tafi China idanshi ya kar budewa shaye shaye da neman mata.
    Bayan ya gama karatunsa nan China wani kamfanin suka dauke shi aiki.sabo da kokarin sa.
   Bayan ya fara wannna aiki ya hadu da wani aboki mai suna Jameel.
  Halinsu yazo daya dana Kamal nan suka zama abokan juna komai tare ya zamana sun hada gida dayama.
    Bayan sun dan kwana biyu da haduwa shine Jameel ya nuna Kamal yana da wata Sana'a wanda in mutun yana yinta zai samu dukiya marar adadi kuma da daukaka.
    Zaka rinka fita kasashan maje kana samu mata kala kala.
    Kamal yace dashi amma baka da hankali me kuma zamu samo mata suyi mana.
    Zaka baka dukiya,motoci,kudi,gida aduk kasar da kake so suna da kungiyoyo kala kala..
     Sude kawai mata zaka kai musu kuma matan suna San wanda shekaran su baikai 30.
Ka ganni nan nafi 5yrs ina wannan Sana'a amma ban taba sanin abunda ake da matanba wannna shine tsarin in kana da sha'awar yi saina kaika.
     Shiru Kamal yyi nadan wani lkc kafin yace ka bari zanyi tunani.


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
 01 Amal fansclub💅🏻🌷



Written by Zeenaseer😘
[26/1 00:03] Zeeenaseeer: © Exquisite Online Writers✍🏻
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
        MARAICHI❣
                 NA
 Zainab Naseer Sarki
     (Zeenaseer😘)



3⃣2⃣


     Dis page goes to u C6 Easlerh matar yya.
Allah ya kawo yara na gari ya biya miki bukatunki ya brki da Angonki duniya da lahira💚❣💚.


⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
     Bayan kwana biyu da faruwar hakan Kamal ya samu abokinsa tare da sanar dashi cewar ya amince da hakan.
    Nan ya umarce shi da fadin ka shirya da yamma zanxo saina kaika wajan ogan mu ku gana.
   Nan kamal yayi masa godiya sannan suka rabo.

    Yamma nayi kamar yanda suka tsara Kamal ya shirya cikin kanana kaya ya kira abokinsa a waya tare da fada masa cewar ya shiryama shi yake jira.

    Baidau wani lokaciba ya bayyana agidan Kamal din nan suka shiga mota Jameel ne yaja motar.
   Shide Kamal yayi zaune yama kasa magana sai kale kale yake.
    Shima Jameel din tunda ya fara driving baiyi maganaba.


    Basu dau lokaciba suka isa wani dan karamin cafe.
   Ga mamakin sa ya juyo ya kalli Jameel.
  Gani yayi ya fita daga cikin motar sannan yayi masa iznin ya fito su tafi.
    Haka ya bude murfin motar ya bishi abaya zowa cikin gurin
   Suna shiga ciki suka fara gaisawa da mutane.
    Shide Kamal bin Jameel yake duk hanyar da yayi.
    Cikin elevator suka shiga tayi kasa dasu.
Sannan suka yi can underground.
Suna fitowa suka bi wani dn karamin corridor.
    Ko ina suka gifta security ne.
Nan suka karasa jikin wani gini wata katuwar koface amma a kulle take.
   Danya tsana Jameel ya sanya sannan abun yayi scans kafin ya bude kofar.
    Wani katan falo suka shiga.komai na cikin falon red nd black ne.
    Zama sukayi kan daya daga cikin kujerun suna jiran kira daga cikin wani daki me jar kofa.
   Shide Kamal babu abunda yake inba kale kaleba dan ganin shi yake kamar dan kauye.
    Basu jimaba wata budurwar yr China tasha jar Riga wanda ita da bbu duk daya suke sai kalan Kamal take shima din ita yake kallo.
     Cikin harshan turanci tace da Jameel ana kiransa.
    Mikewa sukayi shida Kamal suka nufi wannna dakin.
    Ahankali Jameel ya tura kofar.
Komai na cikin dakin White ne ,
Can saman wata kujera suka hango wani dan dattijan mutun sanye da chite suit yana San wine cikin wani Kofi me kyau.
  Jiyowa yayi tare da yima su Kamal nuni da gurin da zaso zauna.
   Ba musu suka matso dan zama.

   Bayan wasu yn lokuta wannna dan dattijo mai suna Leon ya kalli Kamal cikin harshan turanci yace da shi.wannna ne bakon bamu.
    Murmushi Kamal ke yi,
Hannu Kamal ya mikawa Leon suka kara gaisawa.
   Bayan sun  gaisa Leon yayi gyaran murya sannan ya fara magana cikin turanci kamar haka:
   Kamal shine sunan ka,kuma kana da suna me ddi.
   Shide Kamal murmushi kawai yake iyawa.
   Bayan haka ina fatan Jameel yayi maka bayanin yanda abun namu yake.
    Eh yayimin amma inada bukatar sani sosai.
    Ohk babu matsa'
Dama munasan ka dinga samo mana mata amma budurwa mukeso.
    Ko wace guda ka karo zamu baka kudi masu yasa.
   Amma rule na wannna Sana'a ba'a soyayya kuma babu tausayi,ba cin amana kuma babu fita.
  Idan ka amince zamu bada sunan ka wa abin bautarmu.
    Nan Kamal yayi shiru na wasu en lokuta kafin ya ce ya amince.
     Sosai Leon da Jameel sukayi ddin hakan.


Tun daga wannna rana Kamal ya tashi tsaye dan neman matan da zai dinga kawowa Leon.
    Nan ya samu dubara yasa kudi yayi aure daga nan saiya yaudari matar ya gudu.
    Wannan shine ya zama Sana'a Kamal.

     Cikin en lokuta kadan ya zama mai arziki sosai duk abunda yake bukata yana samu dan yanzu gani yake yafi kowa ya taka wanda yaga dama yayi abunda yake so.

Haka rayuwar Kamal taci gaba cikin wannan Sana'a.
     Bayan wasu en watanni Kamal ya shigo garin kebbi dan ziyarar wani frnd dinsa da sukayi mkrnta tare dashi.
    Ranar da ya shigo garin idansa ya sauka akan Sapna. Tun daga lokacin yake murna da kamun da yayi Har zuwa wannan tymdin daya furta mata abunda ke cikin zuciyarsa bayan karya yake.
   Wannan kenan.




       Tun bayan wayar ta da Kamal taketa jin farin ciki Har lokacin da Abba ya kirayeta dan gyaran dakin su.


MUJE ZUWA!!



😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fansclub 💅🏻🌷


Written by Zeenaseer😘
[26/1 14:23] Zeeenaseeer: © Exquisite Online Writers✍🏻
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
       MARAICHI❣
               NA
 Zainab Naseer Sarki
     ( Zeenaseer😘)


3⃣3⃣


     °°°°°°°°°°I dedicated dis page to my lovly once,lubna,swt jiddah nd my durlyn fiyyah💛❣💛


⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
     Bayan ta gama gyaran harta kai bakin kofa zata fita.
    Sapna! Rahma ta kira sunan ta.
   Cak ta tsaya batare data juyoba.
    Dama hakuri zan baki dan Allah ki yafe Mani sharrin shaidanne amma insha Allah hakan bazai kara faruwa.
    Murmushi tayi batare data jiyoban tace Allah ya yafe mana gaba daya.ta fude kofar ta fita ba tare da taji me zata fada bah.
 
    Ita kujera ta samu ta zauna tare da murmushi. Hmmm yarinya kenan dama tayi hakanne dan ta jata ajikinta tasamu nasara a Kansu ita da Shaheeda.

    Tana kumawa dakinsu ta nufa dan kuma duba wayarta ko Kamal ya kira.
    Kusan missed call 5 ta gani.
  Nan fuskarta canza saboda bataji ddin hakan va.
    Da baya ta koma bakin gado ta zauna tana kallan wayar.
    Wani kiranne ya kuma shigowa cikin wayar.
   Da sauri ta daga tare da karawa acikin kun nan ta.
Sallamarma kasawa tayi saboda tsananin farin ciki.
    Daga can daya bangaran yace ina kika shiga tun dazu inata kiranki hrtcntrl.
   Murmushi ta saki mai sauti tare da rufe idanunta.
    Ahankali ta furta Wallahi ina dan wani aikine bata kusa dani ne.
   Ohk va komai.amma bby pls inasan ganinki.
    Toh ba komai da yamma saikazo mu hadu a inda na fada maka.
   Toh my soul sainazo me kike San na kawo miki.
   Duk abunda kaga ya dake dani.
   Shikenan ki huta lfy saina zo din.
   Sannan sukayi sallama.
   Wani irin tsalle ta daka acikin dakin tare da fadawa kan gado.
   Shiru tayi tana kallan wayar Har kwallon farin ciki tayi dan rabanta da kasancewa irin wannan yanayi harta manta.
  Lallai ne hausawa na cewa komai lkcne.yanzu gashinan zata auri wanda ranta yake so kuma shima yana santa kuma tasan Kamal zai kula da ita sosai.
    Sosai tanajin San Kamal cikin zuciyarta.
Burinta shine ya kasance kuda yaushe tare da ita.
   Toh amma wazata tunkara da wannan maganar yanzu tace ga wanda takeso.
   Amma ai akwai sauran lokaci.


      {6:45pm}•••••⚜
  Daidai wannan lkcn Kamal yayi parking motar sa inda sukayi da sapna zasu hadu.
Yana cikin motar ya dauki wayarsa ya kirata tare da fadin gashinan yazo.

   Tana idar da sallah magrib ta danyi light makeup tayi kyau sosai ta sanya hijab dinta sannan ta fita tana rabewa dan kar wani ya ganta.
    Harta samu ta fice daga gidan.sai faman sauri take harta karasa wajan.
   Daga can nesa kadan ta hango motar tasa dan bama kalar ta jiya bace amma ko ba'a fadaba tasan shine acikinta.
    Canza tafiyarta tayi daga saurin da take.
Da yake wajan da haske yana hangota ya fito daga cikin motar ya tsaya yana kare mata kallo.
   Kanta a kasa tana murmushi harta karasa wajan sa.
    Ahankali ta gaida shi cikin muryar ta me sanyi.
   Murmushi yayi kafin ya amsa yace ya gdn ya kk.
   Lfylau wallah.
     Dama haka nake bukata.
   Ki shigo mana cikin motar.
   Aa kabarshi kawai aiba ddewa zanyi ba kawai dama dan mu gaisane.
   Toh shikenan nima bara na futo tunda kema kina wajan.
Karasa fitowa yayi daga cikin motar ya kullo kofar.
Sannan ya jingina jikinsa jikin motar tare da harde hannayansa.yana kallanta.
   Ita kuwa duk kunyarsa takeji dan wani irin Mayan kallo da yake mata.
   Nan sukaci gaba da hirar su ta masoya..
   Sun jima suna hira dan Sapna anji Lov kamar ummieJ😜lol.
Tama manta da wani gida.
   Hannun sa ya sanya cikin aljihunsa tare da fito da wani dn karamin abu.
     Hannun ta ya kamo,nan taji tsigar jikinta ta tashi ga kuma tsoran da taji.
   Da sauri ta daga kanta tana kallansa shima kallan nata yake da murmushi a fuskarsa..
    Dan yatsanta ya kama tare da zura mata dan karamin zobe na gold mekyau da tsada.sannan yayi kissing hannun nata.
   Rufe idanta tayi.
  Saida ya ambaci sunan ta sannan ta bude idan nata tare da kallan gefe still hannun ta na rike da nashi.
    Da sauri ta warce hannun ta ganin wanda ke tsaye yana kallansu.
    Ganin halin data shiga lokaci daya ta janza kamar taga mutu warta.
    Safiya ce tsaye tana kallansu karinta juya tayi hanyar gida ba tare da tace mata komi ba..
     Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un taketa tambata tare da yarfe hannu kamar mejin yaji.
    Shikenan nan mutu yau ina zansa kaina.
    Nan ta durkusa ta fashemai da wani irin kuka.
   Shima durkusa yayi tare da kamo ta.
Da sauri ta janye jikinta daga nashi tana kukanta.
    Ya isa Sapna pls amm sowie ki tsaya kimin bayani banasan ganinki cikin irin wannan halin.
    Shikenan wallah yau kasheni zasuyi.
   Enough mana waye zai kasheki ki kwantar da hankalin ki dan Allah.
   Wallahi bani babu kwanciyar hankali,natafi saida safe ta fada tare dayin saurin barin gurin tana tafiya tana kuka.
   Harta macemai da gani.
   Kafadunshi ya daga alamun ko a jikinsa Shide burinsa ya samesu ga wata star dinma daya gani yanzu.



😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fansclub 💅🏻🌷



Written by Zeenaseer😘
[27/1 12:16] Zeeenaseeer: © Exquisite Online Writers✍🏻
🌳🌳       ⚜        🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
        MARAICHI❣
                NA
 Zainab Naseer Sarki
     (Zeenaseer😘)



3⃣4⃣



❣🌳❣
       Dis page goes to u Aina'un mama,tnx 4d lov,care nd support rwwly appreciate it😘
                       ❣🌳❣


⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
    Gaba daya hankalin ta ya tashi yanzu me Safiya zataje ta fadama su Umma tasan yau kashinta ya bushe.
     Haka tana rabe rabe ta shiga cikin gidan.
Bata tarda kowa cikin tsakar gidan ba,dan haka tayi maza ta shige cikin dakin gabanta nata faman faduwa.
   Bata tsaya ko inaba sai can kuryar dakin.
Safiya na ciki tana canza kaya.
   Tsayawa tayi tare da dukar da kanta kasa hawaye na zuba.
Ahankali ta zame ta durkusa gabanta tare da kara fashewa da wani saban kukan.
    Cikin karkarwar murya take mafana .
   Dan Allah dan Annabi ya Safiya kiyi min rai dan Allah karki fadawa kowa dan Allah.
    Banza tayi da ita ta gama abunda zatayi ta haye gado batare da tace kala! Da itaba.
Ta juya mata bayan taja blanket ta rufe idanunta.
  Lallai ma yarinyar nan,toh inama take zuwa da zata samo irin wannan saurayi hadadde ka kudi wato ni da naje sintiri nan da nan ban samu saurayi kamar nataba.
Shikenan kuwa ba komai wallah kota wani hali saita kwaceshi kuma dole ya aureta.
      Murmushi taci gaba dayi tana jin kukan Sapna amma tayi banza da ita.
 
    Ita kuwa Sapna tana tsugunne a kasa tana ta faman kuka tana magiya wa safiyar amma tayi banza da ita.
Harta fara jin bacci anan amma bata tashiba dan tsabar tsoro.
 
   Har kusan 2am tana nan tana gyan gyadi.ita kuwa Safiya tama manta da wata sapna baccinta taketa faman sha.
   Haka ta mike kafarta duk tayi tsami ta kuma ta kwanta amma Sam ta kasa baccin.
Saida ta jima tana tunane tunane sannan bcci barawo ya sace ta.


Koda suka tashi da safe kowacce shirinta tayi na makaranta suka tafi.
   Hakan yayi mutukar bawa sapna mamaki dan ganin bata gayawa kowaba.
Har aka saukesu suka shiga class.


Husnah taji ddin ganin kawar tata.ganin duk jikinta yayi sanyi ya sanya ta dafata tare da fadin lfy kike kuwa sapna.
    Murmushi ta kwokulo tare da fadin eh lafiya ta qlau.

     Amma naganki haka,pls ki fadamun mana krki buyan komai kawata.nan idanta yakai kan wannan zoban na hannunta.
  Wow! Wannan hadaddan zoban fa muga.
   Ta kamo hannun nata tana gani.
 Gaskiya yayi kyau sapna kode munyi sirikine.

    Murmushi tayi tare da kaimata dukan wasa tace uban siriki kukayi.
   Ga alaman an sa miki zoban kauna.
  Hmmm! Wlh kam.wallah wani hadaddan saurayi muka hadu dashi ke komai ya hada wallahi husny..
Koke saiya burgeki tashin farko irin wayarki yabani kuma yake kirana aci.

     Idanunta ta zaro tare da fadin inkina mahammadan.!
   Wlh kuwa nima ya tashi kaina.jiya kuma dayazo ya bani wannan ta nuna mata zoban.
   Gaskiya tawan.amma kina ganin ba macuci bane ko yn yaudarar nan.
    Hmmm! Allah masani amma hausawa na cewa juma'a da zatayi kyau tundaga laraba ake ganeta..
Nide banga wani Abu marar kyauba.
     Alhmdullh dama haka muke so.Allah ubngiji ya barko tare ya sanya shine mijin auranki ya sa muku albarka cikin wannan al'amari.
    Murmushi ta kuma mata tare da rungume ta tana mata godiya.



    A kwana Atashi ba yauwa gurin Allah yaune su sona zasu fara jarabawan su na waec.
   Soyayya me karfi ta kuma kulluwa tsakanin Kamal da sapna,
Sannan wahalan da take sha ba laifi tadan ragu.
   Kuma gashi sun june da Rahma Har abinci sukeci tare..
     Haka bangaran Shaheeda tana zuwa duba ta takuma kawo mata abubuwan da dama.


    Dayan bangaran kuwa Safiya da Kamal suna shan soyayya batare da kowa ya saniba.
  Sunyi alkawarin aure kuma harta sanar da ummanta za'a sanya rana bayan sun gama jarabawa.
    Bayan zazzafan San da sapna ke yimasa kamar zata mutu.

 

WEDNESDAY❣
     yau basu da paper,dan haka suna gida.bayan Sapna ta gama abunda zatayi ta nufi ban garan Aunty Rahama.
     Tana shiga bata sameta a falon ba dan haka ta fara aikin da zatayi.saida ta gama tas sannan ta nufi dakin Auntyn tata.
    Da sallama ta shiga dakin,ganinta kwance cikin bargo ta lullube.
   Da sauri ta karaso wajanta tare da taba ta.
  Aunty baki da lfy ne.
     Wallahi tunda na tashi da safe kauna kemin ciwo.
    Eyyah kuma baki kara yaya a wayaba Aida kun je asibiti.
    Wallah kuwa duba cikin wancan wardrobe din ko ina da sauri maganina.

    Da sauri ta dauko mata maganin da tace ta dauko mata takuma dauko mata ruwan.
    Da kanta ta bata maganin tasha.tana ta mata sannu.
     Itama godiya take mata.sannan ta mike suka dawo falo.
   Abinci Sapna ta zubo mata suka zauna sunaci suna dan taba hira lokaci lokaci.
Har suka gama sannan ta dauke kwanikan ta dawo.
    Zama tayi kan kujera tana mata sannu.
    Yawwa sapna kinji dana sha maganin Har naji dan ddi.
    Dama mutane ne basa San shan magani amma ni da naji canji zansha magani wlh.

    Nikuwa Sapna ke bazaki fito da mijiba kinsan kuna gama exam yayinku zai iya hada ki Safiya ya aurar..
     Toh ni Aunty nayi mai magana amma Har yanxu shiru yace shi yafi San ayi bikin December.
     Toh amma da ya turo iyayen sa ansan da maganar..
    Hakane kam Aunty dan nasan yaya zai iya zabomin wani wlh.
    Hahahha habade saide bana raye kema zaki samo naki me tsadan musha biki.
     Hakane Aunty Allah da ya zaba mana masu albarka.
    Kullum haka suke hirar su sai sun gama cin abincin daran sannan take tafiya.


         Bayan sunyi sallamata dawo part dinsu ta dauko wayarta.
   Tana dauka ta kira shi. Amma be dagaba ta kuma kiransa amma shiru.
    Hakan ya sa ranta yadan bcce.
Dan haka kawai ta kira Husnah suka fara hirar su.



😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fansclub 💅🏻🌷



Written by Zeenaseer😘
[28/1 21:41] Zeeenaseeer: © Exquisite Online Writers ✍🏻
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
       MARAICHI❣
               NA
 Zainab Naseer Sarki
     ( Zeenaseer😘)


3⃣5⃣


    Yau kusan kwana uku amma Kamal be kira sapna a waya ba.
Kullum cikin kiransa take amma baya dauka,hankalinta ya tashi sosai dan bai taba yimata haka ba.


         Bagan sun dawo daga makaranta ta cire uniform dinta tayi alwala tayi sallah ta gama cin abincinba.
     Wayarta dake kusa da itace tayi kara.
Da sauri ta saki cikalin ta dauka ta kara a kunnan ta batare da tayi maganaba dayn dayan bangaran yace
   "Bbyna ykk"
 Shiru tayi batare da tayi magana Har da maida fuskarta ta shagwaba.
  "Bbyna ko fishi kikeyivda nine?
    Cikin sigar shagwaba tace
"Amma kasan tun yaushe nake kiranka kuma nasan kagani kaki dauka kuma kaki kirana"
    "Pls cwt kiyi hakuri kinji emmatana Wlh wayr na anjeta kuma na manta ban kasheba pls bby am so sowie"
    Murmushi tayi tare da fadin"ix ok😌"
    Yauwa tawan shiyasa bake kara sanki.
   Murmushi takuma yi kafin tace
    "Hubby wlh kaga banasan asamu matsala pls kawai ka turo azo ayi magana kar kuma Abu yaxo kaga ya Abba zai iya bamu matsala"
     Shiru yayi nad'an lkc sannan tace
  "Ohk yanzu yaushe kikesan aturo ayi maganar"
    Taji ddi sosai da abunda ya fada sannan tace
  " Yawwa nawan Har naji ddi sosai wlh,kaga tau Tue, zasu iya zuwa on Fri ko ya kagani".
    "Hakane kinkawo shawara Insha Allah bbyna za'a su zo nima banasan abin ya dau tym kinga ana gama exam dinku sai ayi bikin".
   Dad'i taji sosai da abinda Kamal din ya fada.

     Suna gama wayar da ita,ya sauke anjiyar zuciya sannan yace dole ya kuma samun wasu iyayan karyar ya tura gidn su Sapna agani kamar yanda ya tura wasu na karyar gurin Safiya.


         ⚜❣⚜
  First August 2012❣
        Yaune ranar da ake partyn graduate na makarntarsu ko wannan su sanye suke da dogayan riguna red duk sunsha Makeup sunyi kyau.
    Sai zirga zirga jama'a suke kota ina.
Hall din yasha kyau komai a tsare kida me ddi yanata tashi.
   Can na hango sapna da Husnah sunyi kyau kamar ka sacesu ka gudu suna zaune Suda wasu sauran abokansu.
   Filin rawa kuwa su Safiya da kawayanta ke tashewa sai liki ake musu.

     Anata faman shagali Har bayan magrib sannan suka fara shirye shiryan rabuwa.
    Husnah ce tace da sapna" ko zamu saukeki agida tunda naga kinata jira kuma ba lallai Safiya yanxu zata tafiba".
   "Hakane kam bara na zo mu huce kawai"


      Har kofar gida aka kai Sapna sannan sukayi sallama da Husnah ta shige cikin gida.
   Tana shiga taje tayi abinda zatayi sannan ta janyo wayarta dan kiran masoyinta.
    Lokacin data kira shi yana busy.
Dan haka ta jira ya gama wayar tukun.
   Bayan in mintina kadan ya kirata.
  Da murmushi a fuskarta ta dauki wayar tare da fadin.
   " emmatana an dawo daga sch.din"?
   "Uhmm! Wlh yanxu muka dawo bakajiba duk na gaji"
   "Eyyah kunaxo na miki tausa"ya fada da zolaya.
   Hhhhh dariya itama tayi tare da fadin " sai kazo din ina jiranka".
     Nan sukayi ta hirar Har sukayi sallama sannan ta kwanta Har Lokacin Safiya bata dawo bah.


⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
      Zaune suke shida bash suna hira yanda zasu tsara bikin da za'ayi nan da 3wks.
   Suna zaune gabansu duk kayan shaye shayene kala kala suna sha.
   Bash ne ya hura hayakin taba tare da fadin" malan yanxo kazo zaka had'a gwarama in banda tsabar had'ama taya zakace Har mata biyu zaka aura lkc daya gashi gidan su daya"
     Shima tabar ya zuka sannan ya furzar da hayakin ya jingina kansa da kujera tare da kallan sama idansa arufe yake magana.
   " Aboki kaide ka kalleni kawai nariga na gama samun solution.komai daidai yake tafiya"
   "Uhm! Sannan yace
" wallah shiyasa kake burgeni saman nasan kai shegen Kaine "
    Sannan suka tafa sukaci gaba da hirar su ta yn duniya.


⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
   Su Safiya ana busy ayican ayican bama a zama gida ita da abokanta.sai faman hidima ake dan Kamal ya basu kudi da yawa da zasuyi hidimar dasu.
   Ita kuwa Sapna dama bata da k'awaye da yawa,Husnah ce sai Shaheeda da tazo gidan sai bayan biki zata tafi.
    Suna zaune su uku a dakin Aunty Rahma nata faman hira ana dariya.
   Shaheeda na kusa da Sapna sai kara shigewa jikinta take kamar wanda zata gudu ta barta.
   Husnah ce dake zaune tana gyara wasu kaya da suka siya tace
"gaskiya ni sapna kisan abinda za ai,akanme zamu zauna kullum muna hira event kala biyar wlh nakesan muyi"
    "Toh ni me kikeso nayi Wallahi ni bnma damuba ko kadan"Sapna tace tana karasa tsefe kalbar dake kanta".
     Shaheeda ce tace"ni wallah ya Sapna zan gayyato frnds dina da yawa"
    Rahma ce tace" kinga Sapna ki kwantar da hankalin ki nida nake da jama'a ina me tabbata muku da biki zamuyi na gani na fada na aji"
    Murmushi Sapna tayi sannan ta jingina da kujera tare da fadin"n wallahi duk jiki nama bayamin ddi danji nake kamar wanda akama mutuwa.



😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fansclub 💅🏻🌷


Written by Zeenaseer😘[24/3 23:21] Hussaina: ©EXQUISITE ONLINE WRITERS✍🏻
🌳🌳       ⚜        🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
        MARAICHI❣
               NA
 Zainab Naseer Sarki
      (Zeenaseer😘)


3⃣6⃣

     Dis page goes to u my besty Billy Ghaladanchi.u are ur d best Anty ever. Future ix not smthng u Await!
Its smthng u create!
Plan ur feature in advance coz tat where u spend d rest of ur life:BEST WISHES DURLYN❣💜❣.


⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
     Yau ya kama biki saura sayi daya kowa yana ta faman shirye shirye banda sapna data rame sabo da rashin  safiyar da take kwana biyu duk tayi fari ta rame abin tausayi Shaheeda, Husnah da Anty Rahma ne kawai ke shirye shiryansu.
   Tana kwance cikin dakin kan gado dan zazzabine ajiki.
   Wayr dake kusa da ita ce tayi kara da alama kiranta akeyi.
Ahankali ta dauko ta tare da karawa a kunnan ta dan tasan me kiran bazai huce Kamal ba.
   Batare da tace kala ba ta kara wayr tana sauraran abunda zai fad'a.
   " bbyna ya jikin naki,ko Har yanzu bakya jin ddin ne ko asibiti zamuje"?
   Shiru tayi na dan lokaci kafin tace "eh toh amma kaga yanxu maybe baza barni na fito daga gida ba tunda dare ya dan fara yi"
   Shiru yayi nadan lokaci sannan yace " amma dia naga kamar kina jin jiki pls ki fito kamar zakiyi wani abun batare da kin gayama kowaba saiki fito can bakin titi muje mu dawo"
   "Bakin titi kuma?" Ta fada.
  "Eh mana kinga kar'a ganmu mun fita da daddaran nan amma bakin titi babu kowa"
    Shiru tayi nadan lokaci sannan tace "ganinan zuwa".
   Mikewa tayi jikinta duk babu ddi ta shirya sannan ta fito daga cikin dakin.
   Zaune ta tarda Shaheeda da tana kallo acikin falon.
   Kallan Shaheeda tayi da hankalinta ke kan TV.
  Kawai sai taji kamar ta rungumo dan gani take kamar zata mutu intaje asibitin.
   Batare da ta kuma kallan taba ta cije wayarta na hannunta ta nufi kofa zata fita.
  Kallan ta Shaheeda tayi kafin tace " ya Sapna ina zaki ko jikinne"
   Girgiza mata kai tayi hannunta na rike da mabudin kofar ta rumtse idanunta.
Muryar ta kamar zatayi kuka tace " zan danje kitchen ne na dafa tea na dawo"
  Gyara zamanta tayi tace" amma ya bakya jin ddin fah bara naje na dafa miki"
   Aa ta fad'a "zan iya barshi kawai inna Dora saina dawo inyayi zafi saiki juyo min"
Bata jira abunda Shaheeda zata cefa ta fita tare da jawo kofar.
Jin Gina tayi da kofar tare da fashewa da kuka kamar wanda aka doka.
   Saida tayi me isarta sannan ta fara goge hawayan idan nata.
  Kiranne ya kara shigowa cikin wayar ta amma a silent take,tana kallan wayar Har  ya katse rumtse idanta tayi tana kallan kofar dakin harta fice daga cikin gidan.

    Itama Shaheeda dake  cikin dakin duk batajin ddin ganin tayar tata cikin halin da take sai taji kamar ta bita kitchen din hartaje bakin kofa kuma saita dawo ta zauna tana kallan kofar tana jiran shigowar tata.


    Tana tafiya kamar bataso shikuwa sai faman kiranta yake amma taki dauka kamar wanda bata da jini haka take tafiyar gashi daga gidan zuwa titin da yr tafiya.
     Saida ta kusa karasa Lokacin yana kira ta dauka tare da "Cewa ina kusa da gurin"
  Bata kara cewa komai ba ta kashe wayar taci gaba da tafiya.
   Daga can nesa kadan ta hango motar tasa.
Kai tsaye wajan ta nufa dan su tafi.

     Tunda ya hangota daga nesa ya zuba mata ido yana kallanta.
  Haka ta karo ta bude gidan gaba ta zauna batare da tace masa komaiba dan ko sallama bazata iyaba dan bakinta yayi mata nauyi.
   Kanta ta jingina da kujerar idanta a rufe tana sauke numfashi daki daki.
   Kallan ta yayi tare da danyin murmushi shima bece mata komaiba ya kunna motar suka bar wajan.
    Bayan sun danyi nisa ya kalleta yace "sannu Ashe haka jikin naki yayi amma kikaki gayamin"
    Bace masa komaiba ita sai daukar Ajjiyar zuciya take ido rufe.
   Shima shirun yayi yaci gaba da driving dinsa.


     Bayan kamar 10mins da fitarta Shaheeda taji shiru bat shigo ba,dan haka saita mike ta nufi kitchen.
   Tundaga kofar daki ta hango kofar a rufe amma sai tayi tunanin ko ita ta turashi.
    Ga mamakinta data karasa babu kowa cikin kitchen kuma babu alamun an Dora wani Abu akan wuta.
  Duk da karamar yarinya ce amma saida gabanta yayi muguwar faduwa.
   Da sauri tahau kwallah mara kira tana nemanta soko da loko na gidan.
   Dakin Umma ta shiga ko sallama babu bataga kowa cikin falon bane shiya ta shiga cikin dakin.
Zaune ta gansu saman gado suna duba wasu kaya.
   Ganin yarinya kai tsaye ya sanya suka kalleta tare da fadin "ke lafiya zaki shigowa mutane daki ko sallama babu"
    Kamar zatayi kuka tace " ya Sapna nake nema"
   "Toh kin bamu Ajjiyar tane dama"?
    Jin hakan ya tabbatar mata da cewa bata dakin.
    Ko kulasu batayi ba ta fice daga dakin ta nufi dakin Anty Rahma tana kuka.
    A bude taga part din dan maybe Abba be shigoba sai sauri take kamar zata fadi tace ta shiga cikin dakin.
     Babu kowa acikin falon wanibuban ihu ta kalama Sapna amma bataji ta amsaba.
    Da sauri Rahma ta fito kamar zata fadi ta karaso wajan Shaheeda tana fadin
    " lafiya kuwa Shaheeda kike irna wannan kara kamar wanda aka kwakulewa ido?
   Kallan ta tayi idanta duk hawaye tace " Anty ya Sapna bata shigowa?
    "Eh Shaheeda bata shigoba lafiya de ko? Rahma tavfada tana kallanta.
    Tana kuka tace " toh wallahi ta bata ko kuma an sace ta Amma yaya bata fita da daddare koda kuwa menene dama ance ana satar mutane na shiga uku"
Ta kuma fashewa da wani saban 😰


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fansclub 💅🏻🌷


Written by Zeenaseer😘
[24/3 23:21] Hussaina: ©EXQUISITE ONLINE WRITERS✍🏻
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
                👑👑
                   🌳
        MARAICHI❣
              NA
 Zainab Naseer Sarki
     ( Zeenaseer😘)


3⃣7⃣

   I dedicated dis page to Sis Aenas Tasee'u { Momy's gurl }.bst frnds change wid tym.
But a sister ix d bst frnd dat stays ur bst frnd 4ever.I lov u sis nd always wishing u joyful life.💘💘💘


⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
   Gaba daya Rahma ta kasa gane abunda Shaheeda ke fadi,zama tayi kan kujera tare da fuskntar ta.
  "Kinga Shaheeda ki tsaya kimin bayani gaba daya ban gane abunda kike fad'i"
   Cikin kuka tace "kinga Anty dama kinsan bata da lfy"
  Gyada mata kai tayi alamun Hakane.
  "Toh ina kallo dama ya Safiya bata shigoba,sainaga ta fito kamar ma kuka take,sai na tambayeta inda zataje,saita cemin
" zataje ta dafa tea ta dawo"
   Danace mata "ta tsaya naje na kawo mata"
   Tace dani "na bari yanzu zata dawo".
   " kuma gashi na duba ko ina amma ban gantaba wlh an sace tah"
   Kallan ta tayi da tausayi baganin yanda hankalinta ya tashi lokaci daya haka.
   "Kinga shaheeda bafa yanda za'ayi wani ya shigo Har gidan nan ya sace Sapna,sai dai in wani gurin taje"
   Kallan ta tayi da idanta daya kada yayi jajir tace "amma Anty kigaba yanzu 11pm in zata fita? Kuma tasan halin ya Abba inya dawo yaga bata gida,gashi ba lfy gare tafa"
   "Toh yanzude naji zauna mugani zuwa anjima in bata dawo ba saimu yanke hukuncin daya kamata,tashi muje ki kwanta"
    Da ker ta lallaba ta yanda suka tafi dakin.saida tayita kwantar mata da hankali,gaba daya itama Rahma jikinta yayi sanyi dan tanda sukayi mugun sabo dasu tanajin itama inta rasa Sapna bazata taba jin ddi ba duk da mugun nufin da take dashi a Kansu.
 

Saida sukayi nisa suna tafiya amma babu wanda yake magana acikinsu,ita dama Sapna tunda ta jingina kanta bata kuma cewa komai da idanta a lumshe yake saide hawaye dake zubowa ta gefen su.
    Daidai wani dan karamin clinic sukayi parking motarsu.
   Saida ya kashe motar sannan ya kalleta tare da fadin muje ko,bai cemata komaiba ya bude kofar ya fita.
Zaga yawa yayi ya bude mata side dinta.
  Ahankali ta fude jajayan idanta ta kalleshi tare da maidasu ta rufe.
   Shima kallantan yake kafin yace" pls ki daure mana mu shiga a dubaki kinsan kinajin jiki fah"
   Haka ta zuro da kafarta kasa daga cikin motar tare da fitowa.
 Janyo kofar yayi ya kulle sannan suka jera suka shiga cikin clinic din.
    Kai tsaye wani dn office ya nufa da ita dayake babu kowa tunda suka shigo.
   Tura kofar yayi tare da shiga itama shifan tayi tare da sallama a hankali.
   Mutumin dake zaune kan kujera fuskar sa dauke da murmushi ya mike tare da mikawa Kamal hannu suka gaisa.
   Sannan ya nuna musu guri suka zauna.
Ita de Sapna kanta a kasa ta rasa abunda ke mata dd'i arayuwa.
   Kallan ta mutumin yayi yana murmushi tare da fadin "Amarya ya jikin naki?
    Ahankali ta furta " da sauki"
  "Toh Allah ya kara sauki"
   Nana tamai bayanin duk abunda ke damunta sannan ya bata maganin kuma ya ce za'a mata allurar.
   Nan fa hankalinta yayi mugun tashi dan bata kaunar allura ko kadan.
    Koda ya taso zaiyi mata allurar 'kin bada hannun tayi tana hawaye.
   Likitan ne yace "haba Amarya karki bani kunya mana keda zaki haihu Har Kya gujema allura"
    Juyawa tayi tare da kallan Kamal dake zaune yana kallan su ita da likitan idanta fal hawaye.
    Kai ya gyada mata alamun ta yarda juyawa ta kumayi tare da rufe idan hawayan ya karasa zubawa.
   Ahankali ta shiga tattare hannun rigar tata tare da mika masa hannun.
    Idanunta ta rumtse gama harya juye mata duka ruwan allurar ajikinta sannan ya yi murmushi tare da cewa
"Ba shikenan ba gashi Har angama matsoraciya"
   Gyara hannunta tayi sannan sukayi sallama da Dr.suka fito Har bakin mota ya rakosu.
   Kamal ne ya bude mata ta shiga ta zauna dan kanta yayi mata wani irin nauyi.
   Sannan ya kulle tare da kumawa wajan Dr.
  Kamal ne ya kuma zura hannu a aljihunsa yace "gashi ka kara na gode sosai Allah kara basira"
   Dariya shima yayi tare da ansa yanata faman kara gode Masan.
Sannan suka kara sallama.
    Koda ya koma cikin motar tuni ta dade da yin bacci murmushi ya kumayi tare da gyara mata kwanciya.
 Shima shiga yayi sannan ya dauki wayarsa ya kira bash.
   Yana dauka Kamal yace dashi "guy anfa samu nasara kan yarinyar nan yanzu haka an mata allurar nan da kwana biyu zata farka yanxu tunda tafiya kai zakayi kazo ka dauketa saika tafi bauchi da ita kafin Leon ya aiko a kwashesu duka koya ka gani"
   "Gaskiya ne mutumin baka da wasa muhadu awajan cafe din nan saika banibitan"
  Sannan sukayi sallama ya kashe wayar,kunna motar yayi yabar wajan.


   12pm agogon dake jikin bangon falon Rahama ya nuna,tana nan zaune dan ta kasa baccin ma.
    Sai faman saba da marwa take cikin dakin nata.
   Waje ta fito tana kokarin fita daga part din nasu taci karo da Abba ya shigo a bige sai surutai yake famanyi.
     Bata tabajin haushin halin da yake cikiba Amma yau saida ya bata haushi kota kanshi bata niba ta huce warta.
    Kodabta karasa part din su Umma Har sun kulle kamar ta fashe da kuka haka takeji.
(Lallai sabo turkin wawa Allah Sarki Sapna😪)
    Buga kofar ta shiga yi iya karfinta amma shiru ba'a bude bah,hakan ya kara tun xurata ta kara karfin bugun saida takai kusan 20 mins anan sannan Umma ta bude mata kofar.
    Kamar ta kifeta da mari ta fada cikin tsawa " ina Sapna take kunaji ana bugawa kuki budewa"
    Kallan ta Umma tayi kasa da sama sannan tace "ubanwa kika bawa ajjiyarta?
    Bata kuma ce mata komai ba ta huce ta gefanta ta nufi dakin su Sapna.
   Tura dakin tayi nan ma akulle dan Safiya ta kulle shi.
    Nan ma bubbugawar tahau yi tana kiran Safiya.

   Cikin bacci taji ana kiranta da sauri ta mike tare da Sosa idanunta.
   Safiya! Ta kuma kwala mata kira.
  Mikewa tari da sauri ta bude dakin nasu tare da fadin gani.
    Kallan ta takeyi kafin tace " Sapna tana ciki?
    Ceke da mamaki ta fara girgiza kai alamun bata nan "aww! Aini Nazata dakinki zasu kwana danaga ban gansuba ita da Shaheeda"

    Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un!! Abunda ke fitowa daga bakin Rahma shikenan abunda Shaheeda ke fadi yabtambata.
 
    Umma da Safiya ne suka kalli juna sannan Safiya ta kalli Rahma tace "Anty waime ke faruwa ne?
    Kallan ta tayi tare da "fadin ba aga Sapna ba"

    "Ba'a ga Sapna bah!
Safiya ta maimata maganar kamar ya?
    Nan ta gaya mata duk abunda ya faru.
    Nan da itama jikinta yayi sanyi dan sunsan Sapna babu inda take zuwa inba gidan Anty Naja bah kuma bata gari tayi tafiya.

   Safiya ce tace " toh ina Sapna ta tafi Abu da naga kamar bata da lafiya"
   Anty Rahma ce tace "tabbas batavda lafiya wannan Abu abun dubawane wallahi "

     Ummace tayi tsaki.
Nan suka maido da dubansu gareta dn suji me zata fada.
     "Toh meye abun mamaki aciki dan ba'a ga Amarya a gidan suba,Amare nawane da suke guduwa in basa San auran"
    Tana kaiwa nan ta shige warta dakinta.
   Kallan juna suka kuma yi sannan Safiya ta ceda Rahma "dama Sapna bata San angon nata?
    Aa ta girgiza kai tare da fadin " ko kadan wlh tana sansa mana,nide na kasa gane wannan al'amari"
     Shiru sukayi sannan tace " Sapna ta cemin saurinta sunan sa Kamal ba abokin saurayin ki bane Aliyu?
  "Hakane  abokinsane"
 ta fada

(Dama kamar cema Safiya yayi bashi bane saurayin Sapna bah Amma abokaine su shi sunan sa Aliyu ita kuma ta yarda)

   Anty Rahma ce tace "zoki kulle gidn natafi magani zuwa gobe muga ikon Allah"
    Sannan ta fito daga part din.


Yana karasa a motarsa wajan da zasu hadu da bash wayr Kamal tayi kara kuma Sapna ce ke kiransa.


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fansclub 💅🏻🌷



Written by Zeenaseer😘
[24/3 23:22] Hussaina: ©EXQUISITE ONLINE WRITERS✍🏻
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
       MARAICHI❣
               NA
  Zainab Naseer Sarki
      (Zeenaseer😘)


3⃣8⃣

     Congratulations sis Ummie jay for  concluding of ur sweetest nvl ever
🌵🌵🌵🌵🌵🌵🌵🌵🌵🌵
🏃🏼 TUDUN DAFAWA 💃🏼
🌵🌵🌵🌵🌵🌵🌵🌵🌵🌵
     May god bless u nd more greace to ur elbow,Allah ubngiji ya kara basira da hazaka ya brmu tare ya karemu daga sharrin mahassada.
💘tnx 4being my frnd
💘tnx 4tnking about me
💘tnx 4caring about me
💘tnx 4anytin u did 4me,u shouldn't have but I'm so glad u did.
💘u treated me lyk ur family member.tnkuuuu  very much anyway,ur always in my heart💓
          ❣❣❣


⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
     { pls kuyi hkr nayi mistake inasan na sanya safiya ne ba Sapna ba 🙏🏻}😍

•••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••
     Yana dagawa yaji ta kama mai kuka.
   Murmushi yayi tare da fad'in " lafiya kuwa kike kuka safiya"
    " murya na rawa tace wlh Sapna ce ta bata pls ka tambayi Aliyu ko suna tare"
    "Wannan kuma wani irin maga nace safiya Aliyu fah baya garin nan yana kano kuma sai Thur zai dawo tayama zaki kawo wannan cikin zuciyar ki pls ki bar wannan maganar kude neme ta,nasan batayi nisaba"
   " toh Insha Allah amma abun ne da mamaki babu wanda yasan tama fita daga gidan wallahi "
    "Tafdi Jan Allah ubngiji ya kiyaye kisan mata da yawa suna barin gida jansu kodan wata matsala,amma yanzu nazanyi saurin gaya masa ba dan hankalinsa zai iya tashi Ade kara dubawa ko tana wani wajan"
     Hakade sukayi sallama.
Kamal sai dariya mugunta yake yana kallan Sapna dake gefansa tana bcci.
  A fili yake fadin "saura ke yarinya"


Bai jima da zama agurinba ya hango motar bash ta karaso wajansu.
   Zuge glass din yayi yana lekensa ta cikin motar.
   Fuskar shi dauke da murmushi yace da bash "fito da Allah ka dauke ta ku huce dn ina da abinyi kasan kuwa Har Safiya ta kirani na juyeta.
Kasan de yau Mon pls  nan da Thur ka dawo kasan Kaine Aliyu" ya karashe maganar yana dariya.
    Shima fude motar yayi yana dariya ya fito daga ciki yana fadin " mugu! Mugu!!
   Wallahi baka da tausayi duka biyun zaka dauke musu kenan"
   Murmushi Kamal yaci gaba dayi yana kallan sapna dake kwance.
    Daga yowa bash yayi ya kunce sit belt din ya dauketa cak kamar yr tsana ya nufi motarsa da ita yana fadin "wannan badaban shegenan Leon ba daba sai na muretaha"
     Cikin gidan baya ya kwantar da ita sannan ya kulle kofar ya tawo daidai side din Kamal, y durkuso daidai yanda zasuyi magana yace "toh ni zan huce saina dawo pls nasanka ba wasa saina dawo a kula da komai fah"
   "Ohk" kawai yace tare da yima motar key yayi mai sallama ya jata yabar wajan.
      Shima tashi ya shige tare da janta ya dauki hanyar Bauchi state.


•••Daran babu wanda yayi bccin kirki Har Umma da Safiya dan tunanin su suma ina Sapna ta tafi kowa da abunda yake sakawa acikin ransa.

 ••••{7:15am}••••
     Anty Rahma ce ta fito daga cikin dakinta falonta ta shigo zaune taga Abba yana duba wayarsa.
    Zama tayi kusa dashi tare da fadin "kaiku wa kasan abinda ke faruwa cikin gidan nan kuwa?
     Wayr ya anje a gefe tare da kallan ta da tuhuma r meya faru?
    " hmmm abun,abun mamaki yau awayi gari babu Sapna "
    Duk da yanda yake da Sapna Amma saida ya dan kadu kadan,zaro idanunsa yayi tare da fadin "mutuwa tayi?
    " Wallahi in mutuwace da sauki tunda gawarta na cikin gida,yarinyar daba wata lafiya gareta ba Amma wallahi tun jiya da dare an nemeta sama ko kasa ba'a gantaba"
   "Ba'a ganta bah" shima ya kara maumaitawa.
    "Wallahi kuwa ba'a gantaba gashi ita ba wai guri take zuwa ba kuma ba wat....
   Bata karasa maganaba ta mike tare da dauko wayarta dan kiran Husnah ta tambayeta ko taxo gidan.
   Sau biyu tana kira amma ba'a daukaba sai ana ukun aka dauka bayan sun gaisa.
Rahama ke tambayar Husnah ko Sapna tazo jiya da dare.
    " sapna kuma Anty ban ganeba"
   Nan tayi mata bayanin duk abunda ya faru.
   "Innalillahi wa'inna ilaihir Raji'un!!!" Taketa ambata



😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
 01 Amal fansclub 💅🏻🌷




Written by Zeenaseer😘
[24/3 23:22] Hussaina: ©EXQUISITE ONLINE WRITERS
🌳🌳       ⚜        🌳🌳
🌳                              🌳
              👑👑
                 🌳
      MARAICHI❣
             NA
 Zainab Naseer Sarki
     (Zeenaseer😘)



3⃣9⃣


••••" Amma Anty toh ina Sapna zataje a wannan lokacin gashi dare yayi kuma nasan bata gama jinyar bah"
   "Tabbas Lokacin da Shaheeda taga ta fita batajin ddi wallahi nide wannan al'amari Har tsuro yake bani"
   "Allah de ya kyauta" cewar Husnah wanda itama hankali ta yatashi dan gaba daya tama rasa ya zata kamanta abun ace Amarya saura sati gudu ta bata wannan abun dubawane.
    Sallama sukayi da Rahma tare da fadin sai tazo.


Lokacin da bash ya shigo garin Bauchi kai tsaye wani gida ya nufa wanda yake ba acikin gari sosaiba dan yayi dn nisa da mutane.
     Yana karasawa ya fita ya bude gate da kansa sannan ya koma ya shiga da motar cikin gidan.
    Sannan ya koma ya rufe gate din.
   Saida ya fara zuwa ya bude gidan sannan ya dawo ya dauko ta ya shiga da ita ciki.
   Tun acikin mota ya cire mata hijab din jikinta Riga da wandone na bacci ajikinta dama,rigar iya cinya me dogun hannu amma bata da nauyi haka handanma light blue colour din su.
    Sai kanta data daure da ribbon.
 
 Yana shiga cikin gidan da ita wani daki ya shiga sannan ya bude wani dakin again acikinsa.
   Wata rijiyace akasan dakin Amma bata da xurfi sosai ciki ya jefata sannan ya bita tare da rufe dakunan..
   Ya koma cn dayan part din ya shiga ya tube kayansa ya shiga yayi wanka sannan ya kwanta.


Lokacin da Shaheeda ta tashi daga bcci bataga Sapna ba nan ta kafa wani saban kukan Har Husnah tazo ta sameta tanata faman kuka.
    Da ker Husnah ta lallabata ta ci abinci sannan tayi wanka.
   Kowa acikin gidan anan jikinsa yayi sanyi dan batan Sapna banda Umma daketa faman shirye shiryen bikin ita yanxu ajikinta dan gani take kamar guduwa tayi batasan auran.
   Haka gidan nan ya huni babu ddi dan su Rahma duk basa jin ddi.
  Duk inda Husnah ta sani ita da Sapna sunje ita da Shaheeda amma babu ita babu labrnta.
   Sunyi kuka sosai kuma Har yanzu basu cire rai da itaba dan bazasu taba mantawa danitaba.
    Ranar yini sukayi suna yawo gashi ranarne suka tsara dan ranban IV gashi ba Amarya sai hakura sukayi.
    Koda Kamal ya kuma kiran Safiya tace Har lokacin ba'a ga Sapna ba nunawa yayi beji ddiba kuma suma zasu taimaka da cijiyarta gidan radio da TV hakan bai yima Safiya ddi ba duk da basa shiri da ita amma dn uwa Rabin jiki itama batajin ddi dan ko abinci bata iya ci.
   Gashi ranar laraba za'a fara biki.


Sai kusan magrib sannan Husnah tabar gidan cike da tunanin kawar tata.
    Ita kuwa Shaheeda abincima sai anyi da gaske take ci,haka bata da wani fara ciki lokaci daya duk tabi ta rame ta lalace lokaci daya ta canza kamar ba itaba.
     Koda yaushe idanta akwai hawaye ajikinsa.

    Tana kwance bayan magrib acikin dakin su.
Idanta arufe yake kamar bacci take amma ba bcci take bah duk da ita karamar yarinya ce amma tana da wayo kuma shakuwar da sukayi da yayar tata tasanya gaba daya tafi kowa damuwa.
   Koda aka kira ya dan Asabe aka sanar da  shi be wani nuna damuwarsa  akan taba saboda Umma ta shiga tsakanin su.
        Sallamar su Nana ce nasanyata mikewa ta rugu da gudu ta fada jikin Aunty Ummi tana kuka.
    Da ker itama ta lallasheta tayi shiru da yake duk Safiya takura ta sanar da kowa shiyasa suka sani kowa mamaki yake gashi an rasa rama ina za'a fara neman tah.
      Haka  sukaita jimami suna lallashin Shaheeda.
  Ba laifi gida yadan fara cika amma babu walwala sosai sabo da rashin Sapna.
  Dagin su ummane kawai ke abunsu batare da sunji wani abuba danasu dama sun tsani su Sapna.


Har Lokacin Sapna na cikin rijiya bata farkaba.dan sai gobene zata farka a yanda likitan ya fada.
    Dan Lokacin daya cillata ciki saida kanta ya fashe haka yayita jini harta tsaya dan kansa.
 


    •••• TUESDAY ••••
  Washe gari gida ya fara cika da mutane sai hidima ake,kowa da abunda yake yi.
   Masu jimami sunayi haka Shaheeda na gefe abun tausayi.


Tunda safe da bash ya fita be kuma dawo wa bah.
   Ita kuwa Sapna nacan akwance.
  Ahankali ta fara motsa hannunta harta motsa kafafunta,sannan ta bude idanta tana kallan gurin,da sauri ta mike zaune tana dafe kanta tana kallan wajan.
    Saida ta karema rijiyar kallo sannan ta fara kallan jikinta.ahankali ta fara tuna abunda ya faru tsakaninta da Kamal.
      Kenan Kamal yaudarata yayi tabbas yaci amanata,kara fashewa da kuka tayi ga kanta dake mara wani irin azababban ciwo da yake mata.
    Yanzu ta inama zata fara neman hanya fita daga nan,gurinwa zata,ta ina zata fara fita.
   Mikewa tsaye tayi tana kallan saman gurin ba wani nisa gareshiba amma taya zata takala ta haura ta fita.
   Juwa taji tana dibarta komawa tayi ta kwanta awajan tare da rufe idanta tana ci gaba dajin ciwan data take ji.


 Gidan su Amarya anata faman shirin tafiya kamu,dan mutane da yawa basu damu da wani Sapna bah.
    Nana ce ta lallaba Shaheeda aka shiryata Har aka mata kwalliya.
   Itade gaba daya Shaheeda batasan zuwa ko ina burinta abarta ta kwanta ta huta ko taji ddi dan in tana cikin jama'a ana cikin hayaniya bata jin ddi.
   Haka aka gama shiri aka fita zuwa wajan kamu.
   Aunty Ummi ce kawai bata jeba,waya ta dauka ta kira dan Asabe.
   Lokacin daya shigo gidan zama yayi kan kujera yana kallan tah.
   Shima shi take kallan,
Kafin tace "yanzu kai dan Asabe abinda kake kana kautawa,yanzu bama aa kirani ka fadamin 'batan yarinyar nan ba,kuma tunda mu ba'a kusa mukeba,kamata yayi kaine uwarsu kaine ubansu tunda Kaine Baba, Amma sabo da Allah baka damu sa itaba,kuma da ba haka kake bah"
 
   Shiru shima yayi nadan lokaci kafin yace "kinga yanzu kamar Sapna sai an wani tsaya ana bata lokaci akanta,kinga yanzufa auranta za'a yi,ita tasan inda ta tafi kuma zata dawo,so take ta 'bata mana sunan gida kawai".

  Cike da mamaki take kallansa " haba dan Asabe yo ai ko wanine ya fadimin ka yi wannan furuci bn yarda Amma da bakin kake furta irin wannan, an bawa yarinyar nan kyakyawa r sheda bamata fita sosai kuma ba wani ta saniba.sabo da Allah amma kake irin wannan magana"
 
 "Toh gaskiya ni bani da abunda zanyi kuma" ya mike ya fice daga dakin.
   Baki ta kama tare da fadin"anyah kuwa! "
   Dan abun da mamaki ace dan Asabe da irin wannan.
  Addu'a tayi, tayi tare da fadin "Allah de ya bayyana mana ke yrnan.


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fansclub 💅🏻🌷




Written by Zeenaseer😘[24/3 23:05] Hussaina: ©EXQUISITE ONLINE WRITERS
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                 🌳
      MARAICHI❣


4⃣0⃣


  Tana nan kwance cikin rijiyar wani irin yinwa da Ciwan kai ke damunta gashi gaba daya jikinta babu wani kuzari.
    Ahankali ta kuma mikewa zaune tana cije baki,kallan gurin ta shigayi tana tunanin ta yanda zatayi ta haura ta fice daga gurin.
    Bataga wani Abu da zai iya taimaka mata ba,hakanne ya sanya ta kuma fashewa da kuka😭


    Bayan bash ya dawo daga yawan daran sa yana kokarin shigowa gidan wayar shi tayi kara.
   Daukowa yayi tare da murmushi dan Kamal ne ke kiransa.
   "Ya akayine Ango?
Lafiya de ko?
   " yeh ! Lafiya babu wani damuwa, ya mutuniyar ta farka kuwa?
  "Taf! Aeni Wallahi na ma manta da ita"
  "Amma kaide Wallahi baka da mutunci to meye amfanin tafiyar taka?
  " am sorry yanzu nasan ta farka bari na kai mata abinci"
   Sallama sukayi sannan ya shiga cikin gidan.
  Kai tsaye gurin da taje ya nufa,yana zuwa ya bude ya leka gurin.
  Kwance ya hangota,dariya yayi tare da kiran sunan ta.

   Ita kuwa tana kwance sai hawaye ke zubowa daga idanta dan batun kuka me sauti babu shi.
   Ahankali ta dan d'ago jin an ambaci sunan ta.
  Kallan shi ta shifayi dukda bata gane shiba kuma bata ganin shi sosai tasan ba Kamal bane asalima bata taba ganin shiba.
     Ledar dake hannunsa ya jefa mata tare da barin wajan.
   Daidai fuskarta ledar ta sauka,kasa motsi tayi kawai kallan ledar take still hawaye  wani nabin wani a fuskarta.
   Da ker ta iya yinkurawa ta tashi ta janyo ledar dan in bata Ciba yinwa zata iya mata illa.
   Meat pie ne da lemon gwangwani guda daya sai ruwan roba.
  Hannun ta sai bafan karkarwa yake ta sa hannu ta dauka takai bakinta,nan ta shiga ci kamar mayin waciya.
  Tanaci tana karkarwa harta cinye komai ta shenye ruwan lemonne kawai ta kasa sha.
    Bayan ta gama sha ta dan jingina da bango tana numfashi ahankali tare da lemshe idanta sai lokacin ta danji karfi a jikinta.



••••••Yaune ranar da bash zai koma kebbi dan haka ya gama duk shirye shiryan sa kuma kwana hudu zaiyi sannan ya dawo.
    Dan haka anan zai bar Sapna ya dauko wanda zaina kula da ita yana bata abinci arana sau biyu safe da dare.
     Haka ya gama duk abunda ya kamata sannan ya bar Bauchi.


Lokacin daya karasa kebbi bayan yayi wanka yaci abinci shiryawa sukayi suka nufi gidn su Sapna da yamma.
    Suna kara sawa suka  yi sallama nan aka basu damar shiga cikin gidan.

   Gida kuwa ya cika da in biki,wasu na shagali wasu na alhini.
   Safiya ce tayi musu iso Har cikin gidan dan lokacin ma Husnah da Aunty Rahma na dakin su Ummi.
    Bayan sun gaisa da mutane bash ya fara kukan munafunci ya kuma nuna yanda ya damu da ita sosai.
Koba komai mutane da yawa sun yarda dashi.
   Amma banda Husnah da take mai kallan munafuki.
   Amma gani kowa ya yarda dashi yasa itama batace komaiba.
  Ba laifi ya bawa mutane tausayi kuma da yawa wasu sunyi kuka wasu ko sun tausaya masa sun kuma tayashi addu'a Allah ta bayyanata ko ya bashi mace ta gari.
    Amma shi yace duk inda Sapna tace zai jirata Har lokacin da zata dawo.
   Haka mutane sukayita shima sa albarka dn ganin shi mutumin kirki.


Bayan sun koma gida zama sukayi sunata dariya wa yn gidan su Sapna dan sun daukesu kamar mahaukata.

      Husnah ce ta kalli Anty Rahma tare da fadin "yan Anty shikenan muda Sapna Har abada kenan" ta karashe maganar tare da share kwallar da tataho mata.
   " toh! Husnah kawai Allah za'a mikama al'amarin nan shi kadai yasan inda take kuma Insha Allah zai kuma maidota garemu"
   Hakade sukaita tattaunawa a tsakanin su.


        Tana kwance ta rasa abunda ke mata ddi dan burinta kawai ta fice daga gurinnan.

  Bayan sallar magrib tana kwance tayi shiru taji kamar an cillo Abu.
   Mikewa tayi da sauri tare da fadin dan Allah malam inasan nayi sallah kuma nayi bahaya.
   Cak ya tsaya dan shima tunda yaga yarinyar yaji ta burgeshi,bara ya taimaka mata ko yasamu ya rage wani abun da ita.
  Murmushin mugunta yayi tare da dawo wa baya ya leka yana kallanta.
   Kafin ta kuma cewa"ka taimaka dan Allah "
   Ba tare da yace mata komaiba ya bar wajan.
   Yana tafiya tayi maza ta nemo wani karfe data gani a gurin dan karami dauka tayi ta sakashi a gashin kanta sannan ta tsaya tana kallan hanyar.
    Bayan yn mintina kadan da barin gurin ya dawo hannun sa dauke da katuwar igiya.
   Cilla mata yayi tare da fadin kama.
   Ahankali ta shiga ja ta fara takawa tana hawa,shima yana taimaka mata Har ta kusa zuwa daf da gurin ya wayar shi tayi kara kuma tabbas yasan bashne ke kira.
  Sakinta yayi ta koma da baya ta fada 'kugunta ya bugu da karfi ta saki wata kara.
   Daukar wayar yayi tare da fita daga cikin dakin.
   Bayan sun gaisa yake tambayarsa da fadin babu wata matsala.
   Shima ya shaida masa babu komai.

Komawa yayi gurin zamansa tare da fadin "kai gwara duk abunda yakeji game da yarinyar nan ya danne dan karma wata matsalar ta faru yasna halin Kamal sarai.
   Kulle kofar yayi tare da fita daga gurin ma gaba daya.

 Tana kwance tanata jin zafin gurin data bige danji take kamar bazata ita kara tafiyaba.
   Tanajin lokacin daya kulle taji wani saban kuka da bakin ciki ya ziyarceta dan ba haka tasoba.
   Saida tayi me isarata tasan ita yanzu shikenan ita da rayuwar farin ciki,maybe ma kasheta za'ayi dama tasan rayuwar ta bata da wani amfani.
   Wata zuciyar ce tace da ita" kar kiyi sa'bo Sapna karfa ki manta duk inda kike Allah yana tare dake kuma zai amsa miki addu'a ki aduk lokacin da kika rokesa,karda kiyi kasa a gwiwa ki nemi taimakon Allah Insha Allah zaki samu kuma kisa aranki wannan rayuwar da kike jarabawace ki dage ki cinyeta"
   Murmushi tayi kuma tabbas taji ta samu kwarin gwiwa nan ta fara tofa addu'a a gurin data bige.
   Masha Allah tadanji ddi sosai. Mikewa tayi daker ta kama igiyar ta kulle samanta sosai saida ta danyi kauri sannan ta rinka cillata bata kama abin fanfon dake dakin.
   Ja ta rinka yi Har saida taji ya zauna sosai.
   Murna ta fara Har tsallan ddi tayi.sannan ta kama ta fara hawa tana addu'a tana rumtse ido duk da hannun ta na mata radadi Amma haka ta jure harta kusan kawo wa..
  Nana ta ji kamar abin ya fara kun cewa.juyawa tayi ahankali ta leka kasan taga da dan nisa dan tasan ta fada ba karamin ciwo zatajiba.
   Rumtse idanta tayi tana karanto  addu'a har ta kusan kawowa tana isowa ta riko bakin rijiyar tare da karasa fitowa.
    Tana karasa ta fado waje a raren tana kallan rufin dakin tana sauke lumfashi sama sama tana farin ciki.


Shikuwa me gadin Sapna bayan ya koma ya zauna yayi tunanin ai kamar yabar igiya a gurinta kar kuma tayi dabara da ita ta fito da sauri ya mike tare da tafiya dakin dan dauko igiyar.

  Tana kwance a kasa tana maida numfashi taji karan tafa kofa da sauri ta mike tana kallan cikin dakin,gashi babu wata kusurwa da zata buya,dan babu komai a dakin sai sick da wani dan karamin window daga sama kadan sai rijiyar.
   Gaba daya hankalinta ya tashi jin kara bude kofar da za'a yi.
    Yana budewa ya murda zai shigo......



😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
 01  Amal  fansclub  💅🏻
🌷



Written by Zeenaseer😘
[24/3 23:23] Hussaina: ©EXQUISITE ONLINE WRITERS
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
       MARAICHI❣
                 Na
 Zainab Naseer Sarki
     (Zeenaseer😘)


4⃣1⃣


•••••••••Gaba daga hanakalinta yayi mugun tashi tama rasa yanda zatayi sabo da tsoro.
    Harya sako kafarsa sai kuma yaji kara buga gate daga waje.
   Da sauri ya maida ya kulle ya fice daga gurin.
  Wata sassanyar Ajjiyar zuciya ta ajje tare da jingina ajikin bango.
   Kallan window take tayama zata haura ta sauke glass din wajan gashi tsayinta bazai kaiba.
   Matsawa tayi kusa da gurin tana kallan tsayin wajan.
   Wata dabarace ta fado mata.
  Gurin sick din ta nufa nan ta sauke abin faffan sannan ta dauko makarin gurin da yake yana da dn tsayi.
    Ahankali ta jan yoshi har wajan.
   Sai faman nishi take.
Hawa kai tayi tana tangadi kamar zata fadi.
   Sannan ta dage kafafunta ta kamo abin Glass din cikin sa'a kuwa ta sauke guda biyu dayane kawai ya rage, shima dagen tayi ta ciroshi nan abun ya karyo ta subuce ta falo Glass din yayanke ta ahannu nan ta kwala wani irin ihu,zafi takeji sosai da radadi ga kuma haushin abinda zata takaladin ya karye.
Kuka ta zauna tanayi sosai.
    Da ker ta mike jikinta duk ya bace da jini Dan yankan sosaine sai azaba yake mata.
    Daker tana tsale har hannunta ya kamo wajan a azabar da takeji sai faman kuka take harta yi sa'ar saka dayan hannun sannan ta haura ta haukan window inda zata fada ta baya.
   Da yake dare ya farayi ta leka babu komai agurin sai ciyayi da duwatsu.
Nan ta fara addu'a Dan gurin da dn nisa haka ta rumtse idanunta ta fada.
  Allah ya taimaka bata bigeba.
   Tana fadawa ta mike tare da saka gudu batasan hanyaba kawai itade gudun take tana waiwaye Dan kar abiyota.
   Gudu take sosai Dan gidan yayi nisa da gari burinta itama ta shigo cikin garin ga hannunta sai jini yake tana tafiya juwa Na daukarta.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
   Sai faman saba da marwa take cikin falon su tana kallan agogo,
   Wayarta ta kuma janyowa tare da kirnsa Dan ya jima be dawoba kuma har yanzu yaki daga kiranta.
   Cikin sa'a tana fara ringing ya dauka.
   "Ka kauta kana ina tun dazu ina kiranka kaki dagama kiran nawa bare kaban amsa"
   Murmushi yayi tare da fadin"amma kinsan Na gaya miki yau ina da meeting kuma zandau lokaci bn dawo bah"
   "Toh amma wannan wani irin meeting ne tanzufa kaga 10:45am amma kace meeting"
   "Ohk! Baki yarda dani kenan bah, good!"
   Kashe wayar yayi tare da jefata kujerar dake gefan sa yayi tsaki.
 Afili ya fadi "mutun sai shegen kishi ka rasa abunda zatamin inna dawo din ina dalili"
   Tsakin ya kuma yi yana kallan titi dan tuki yake.fahad kenan☺

   Da sauri yaci burki ranshi a bace,tsaki yayi tare da fude motar ya fita afusace.
    Ita kuwa gaba daya ta rikice ga jini ya zuba sosai sai layi take.
    Yana karasowa wajan ya nufi wajan ta tare da fadin "ke wace iriyar mahaukaciyace bakya gabin hanyane yanzu da......
  Bai karasa maganarba ta tafi luuuuu! Zata fadi.
Da sauri ya tarota ta fada jikinsa,sai lokacin ya lura da jinin dake zuba ajikinta da sauri ya dauketa yana waige waige ko wani ke binta amma harya sakata cikin mota baiga kowaba,
   Zaga yowa yayi tare da shiga cikin motar ya figeta da karfi ya nufi asibiti da ita.

  Mamaki sosai yake ganin yarinya karama a wannan lokacin gashi tana cikin wani hali.
 " ko daga inah take,er gdn wace waye ya biyota"
   Gabaya bashi da amsar wannan tambayr saide inta farka in tana raye.
    Da wannan tunanin ya karasa asibitin da sauri ya daukota ya nufi ciki da ita.da sauri aka amsheta aka nufi emergency da ita.
   Shima gaban  rigarsa tadan bace jinin.
   Da kamar zai tafi saikuma ya tsaya.
   Nan wata nurse tazo ta sameshi tare da fadin "tana da bukatr jini nan da 30mins inba hakaba zata iya rasa ranta dan ta zubar da jini da yawa"
   Shiru yayi nadan lokaci kafin yace" toh nawa ake saidawa asaka mata"
     Nan ta sanar dashi sannan ya bata numb yace gashinan sauri yake zaije gida duk abunda ya kamata ayi anan ya mika mata card dinsa sannan ya fita.
   Sai kallan jikinsa yake yana tsaki dan baiji ddin hakan bah.
   Nan ya shiga motarsa ya nufi gida da yake ba nisa daga nan.


Yana karasawa me gadin ya bude masa get ya shiga yayi parking motr shi sannan ya fito ya nufi cikin gidn dn ya gaji sosai.
 
    Da sallama ya shiga cikin falon.
   Ido biyu sukayi da ita tana tsakiyar falon a tsaye tana kallan sa ta rike kugu ta gama ciki saura kadan ta fashe.
   Nan idanta yakai kan jinin dake jikinsa.
   Shikuwa ko a jikinsa hanyar dakinsa ta nufa dan bashi da tym dinta.
    "Dakatah! Me kake nufi? Kaje kakai wannan lokacin a waje kuma ka dawo bakamin bayaniba ka shige.wannan jinin daga inah?"
 Ta kara she maganar tana nuna jinin da hannunta.
   "Dama ni dankine kenan,da duk inda naje saina miki bayani ko uwata?"
    Tabayarki nake ya daka mata tsawa.
   "Ke wace iricene,ko kina da tabin hankali ne?"
   Shima yana maganar yana nuna kanshi.
   Kuka ta fashe tare da cewa "tabbas ni mahaukaciya ce akanka fahad,kuma saika gayamin wannan jinin mene wallahi"
   Ta karashe maganar tare da kamo 'kwalar rigarsa.
   Fige hannunta yayi tare da kwada mata mari.
   Zaiyi magana wayrshi tayi karanan,yana huci ya zaro wayar a aljihunsa tare da karawa a kunne.
   "Assalamu Alaikoum.
Dama nurse da aka kai patient asibiti"
   "OK INA jinki"
  "A gaskiya duk jinin da aka gwada baiyi daidai da natanba shiyasa Na Kira ka kuma muna bukatarshi da gaggawa"
   Shiru ya danyi kafin yace" ohk bara naxo a auna nawa sa'a saka mata"
   Sannan sukayi sallama.
   Kallan ta yayi tana tsaye itama shi take kallan dan jin yana magana da mace.
   Juyawa yayi zai fita daga dakin.

   Da Sauri tasha gabansa tare da fadin wallahi bazaka fita daga gidan nan bah.
 Wata shegiyar za'a sakawa jinika ita tama isa"
    Ranshi a bace sabo da abunda Salma take ya fara isarsa.
   "Ki bani hanya Na huce kona ballaki wallahi"
   "Kan ubancan Fahad ni zaka karya akan wata karuwa to wallahi yau ko kasheni zakayi baza fita daga cikin gidan nan bah ko wace shegiyarce saide ta mutu amma babu inda zaka"


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
 01 Amal fansclub 💅🏻🌷



Written by zeenaseer😘
[24/3 23:23] Hussaina: ©EXQUISITE ONLINE WRITERS
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
       MARAICHI❣
                NA
  Zainab Naseer Sarki
      (Zeenaseer😘)


4⃣3⃣

•••••• juyowa tayi tana kallan shi tare da fadin "waye kuma ba lafiya?
    yana danna wayar hannunsa yace " Wallahi wata baiwar Allah ce"
   Nan ya gayama duk abunda ya faru.
   Ta tausaya mata mutuka sannan tace"ko yr gidan waye baiwar Allah ko ina iyayanta?
   " toh wallahi ga shinan de yanzu inna gama cin abincin saina je "
   "Gaskiya kam bara na shirya saimu huce tare Nima na dubatan"
    Nana tayi maza ta hada masa abinci ya kamaci,ita kuma ta hau shirya abincin da za'a kai asibitin.
    Bayan ta gama ne ta nufi daki dan ta shirya.

    Basu dau lokaciba suka kammala duk abunda zasuyi suka fito dan tafiya asibitin.

 
  Lokacin da suka isa asibitin kai tsaye dakin da Sapna take suka nufa dayake yasan wajan.
   Da sallama suka shiga dakin.                       
     tana kwance saman gado a kwance kamar bacci take amma idanta biyu.
    Sallamarsu ce ta sanyata motsawa daga kwancan da take juyawa tayi tana kallan wa enda suka shigo din.
    Suna hada Ido da mummy ta sakar mata Murmushi tare da matsowa wajanta ta zauna tana mata sannu.
   Da ker ta iya bude baki ta gaidasu.
   Sannan sukayi mata ya jiki.

  Fahad kuwa tunda suka shigo ya juya yafice daga dakin danshi ko kadan yarinya batamai bah duk da tana da kyau.

     Mummy CE ta kuma matsawa wajanta tare da dafata " sannu kenji er nan ya karin saukin jikin?
   "Alhmdullh" ta furta kanta a kasa.
   "Sannu kinji Allah ya baki lafiya yanzu tashi kiyi wanka bari naje Na dawo"
   Mikewa tayi ta fita waje

  Itama Sapna tashi tayi da ker ta nufi toilet din dan gasa jikinta da ruwan dumi.

  A daya daga cikin kujerun  dan corridor dakin ta hango Fahad din yana danna waya.
   Karasawa wajansa tayi tare da zama sannan ta kalleshi.
 "Fahad ya kamata ka tsallaka ka samowa yarinyarnan rigar da zata sanya inta fito daga wanka."
   Shiru yayi bece komaiba yaci gaba da abinda yake.
  Cikin bacin rai ta kuma cewa" magana fah nake maka Fahad kana jina"
  Kamar zaiyi kuka ya bata rai tare da fadin "haba dan Allah mum ya kuma haka,taimakonta ne kuma nayi yanzu kuma kayan sawarma ni zan siya mata,kawai inta ci abinci ki kwaso mana kayan mu tafi,ko ita bata da dangine"
  Tunda ya fara maganar take kallansa da mamaki dan tasan ba haka yakebah,yana da San taimako amma akan wannan yarinyar ta kasa gane kasa.
  "Kaga Fahad nifa bana San kana irin wannan, kaida kake da taimako amma lokaci daya ka canza yanayinka,duka yarinyar nawa take da zaka dau karan tsana ka dora mata,ka dubeta abin tausayi ni Dama iyayanta zasu bani ita"
    Kallanta yayi tare da fadin "kinga mum nasan halinki pls kibar wannan maganar bari na je na siyo mikin"
 Batare da yajira me zata ceba ya mike ya fice daga gurin.


    Lokacin data koma cin dakin,Sapna bata fitoba dan tadau lokacin dan basa jikinta,dan taji ddin hakan sosai.

   Zama mum tayi kan kujera tana jiran fitowar.

   Bayan yn lokuta kadan ta fito daga wanka tare da zama kan gadan ta rufe jikinta da blanket din tadan shingida tana maida numfashi dan sanyi da take danji.

   Kallan ta mum take dan mugun tausayinta take.
  Ahankali ta mike tana mata sannu ta hada mata tea da abinci sannan ta umarceta data tashi taci.
   Shiru tayi tanajin abinda take fada.ahankali ta Mike tana kallan ta.

   Ta sowa tayi da Murmushi a fuskarta ta zauna gefanta tare da mika mata tea din.
  " maza kisha kinji ko kya ji ddin cikin ki"
   Ammasa tayi tana kallan ta dan ta tuna mata da mamanta.Allah Sarki uwa me ddi.
   Hawayene suka shiga saukowa kn kumatunta.
   Ahankali take shan tea din harta shanye duka.sannan ta mikawa mum cup din.
  " yawwa kin kauta tunda kika shanye saura kuma abinci ko?
    Shiru tayi nadan lokaci kafin tace " aa yanzu na koshi saide zuwa anjima"
Tana kaiwa nan a maganar ta koma ta kwanta tare da lullubewa.
   Matsawa tayi kusa da ita tare da shafa mata sumar kanta.kamar karamar yarinyar da akesan a saka tayi bacci.
   Gaba daya tama kasa baccin tama rasa wani irin farin ciki take ciki,tunanin mamantah shine ya dawo mata sabo.
   Tabbas batayi rayuwa me ddiba,kuma bata fatan ta kasance ahaka.
   Uwa uwa! kenan gaba daya tataso batare da tasan ddin uwa.
  Yau ita da ake takurawa,ake kora,ake kyara,wanda ba'a kauna.
  Itace kamar saurauniya akema haka dan tasamu farin ciki.lallai tayanda komai da lokacin sa.
    Allah Sarki rayuwa. Kuka take fama yin amma maras sauti.
  Taji tana San rayuwa da mum Abu gudane bata kauna wannan kuwa shine Fahad..
Ko kadan bata kaunar sakashi cikin idanta.
  Tabbas zuciyar ta gaba daya ta mallakawa Kamal, shine farin cikinta,shine namijin data faraso arayuwarta kuma bazata dena sanshiba har abada.
   Tabbas Kamal ya yaudareta amma hakan besa taji ta tsane shiba,tana kaunarsa sosai kuma har kullum bata da burin daya huce ta aureshi.



😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
 01 Amal fan's club 💅🏻🌷



Written by Zeenaseer😘
[24/3 23:23] Hussaina: ©EXQUISITE ONLINE WRITERS
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                 🌳
      MARAICHI❣
             NA
 Zainab Naseer Sarki
     (Zeenaseer😘)


4⃣2⃣


••••••••••"Salma ki bani hanya Na huce kar ranki ya bace na gayamiki"
    "Hmmmm! Nima na gaya maka kome zakayi kayi amma na bazaka fita bah"
    Kallan ta ya tsayayi da mamaki tamkar mahauciya haka take wani lokacin.
Juyawa yayi ya shiga dakinsa bayan mintina kadan ya fito batare da ta ganshiba ya sama kofar dakinsa key sannan ya zagaya ta baya kofar shiga garden ya bude ya fice ya barta anan tana faman huci.
    Jin karan motane ya sanyata bude kofar da sauri kafin ta gama fitowa ya fice da gudu daga cikin gidan.
   Nan da nan me gadi ya maida kofar ya kulle tare da sanya key dan haka Fahad ya bashi umarnin yi.
    Da gudu ta koma cikin gida ko dankwali babu akanta ta dawo da key din motar ta tare da shiga ta kama kwalama me gadi kira danya bude mata.
   Amma yayi banza da ita kamar badashi takeba dan Fahad yace karya sake ya bude mata gate.
   Barin kofar gidan yayi gaba daya dan karta mai rashin mutunci.
    Wani irin kuka ta fashe dashi ga wani irin bakin ciki da yake cinta.kamar ta mutu ta huta haka takeji.
    Gashi tana san bin bayan Fahad amma yanzu tasan yayi mata nisa.
   Wani saban kukanne ya kwace mata dan shine kadai abunda zatayi zuciyar ta tadanyi sanyi.


Shikuwa yana fita daga gidan sai faman sauri take Dan Salma ta bata masa lokaci.
Yanata faman gudu harya isa aaibitin da sauri ya fito daga motar yana neman layin nurse din nan dan ya ganta.
   Tana dauka ta sanar masa inda zai sameta.
  Nan yayi saurin zuwa suka hadu.
  Jinin sa suka dauka da sauri sukayi test cikin sa'a kuwa yayi daidai.
   Nan suka nufi dakin da aka kwantar da Sapna dan bata jinin.

    Tana kwance an sanya mata drip a dayan hannunta sai faman bacci take an gyara mata duk inda taji ciwo fuskarnan duk ta rame abun tausayi.
    Gadn kusa da ita aka nuna masa ya kwanta.
  Matsawa yayi yana kallanta da kuma jin haushin bata mata lokacin da tayi danshi en badan yana da tausayiba tun acan zai yanda ta yayi tafiyarta.
   Kwanciya yayi badan San ransaba.nan akayi abinda  ya kamata aka fara sanya mata jinin nasa.
   Idanunsa ya lumshe dan muguwar gajiyar da yayi gaba daya so yake ya watsa ruwa ko yaji sanyi,tsaki yaja tare da juyo da kansa yana facing fuskarta.
     Dauke kansa yayi tare da kuma yin tsaki.


^~^~^~^~^ [ 1:32am ]~^
      Sai lokacin aka sallameshi.
   Nan ya shiga motar shi ya nufi gida.
 Koda ya koma gidan har lokacin Salma na cikin mota azaune tana jiran dawowarshi.
    Bayan yayi parking jikinshi duk babu ddi.cikin gidan ya shige batare da ya kuma kallan inda takebah.
   Kai tsaye dakinsa ya nufa ya shiga toilet.
Bayan yayi wanka ya gyara jikinsa ya fito sai kamshi yake.
   Kitchen ya nufa ya hada coffee sannan ya hada sandwich dinsa taci ya koshi ya koma dakinsa tare da yima dakin key ya kwabta.

   Bayan ya kwantane ta fito daga cikin motar ta shigo cikin gidan.dakinsa itama ta nufa tare da murdawa amma ta jisa a kulle dan yasa key.
    Dan haka dakinta ta koma duk da itama jikinta yayi sanyi.
    Koda ta kwanta kasa bccin tayi,sabo da hankalinta ba'a kwance yakeba.
  " Lailai Fahad Neman mata yake.toh amma meyasa yake irin wannan?
   Kashenima yake sanyi"
   Nan ta kuma fashewa da wani kukan.
   Yanzu ita ya zatayi bata burge mijinta,baya nuna mata kulawar data dace.
    Tana da ranta Fahad ya sakawa wata jinisa tafdi Jan,lallai kuwa inhar ta kamata wallahi saita kasheta dan bata isa tayi rayuwa da jinin fahad ajikin taba.
    Gaba daya takasa zaune ta kasa tsaye,daga can ta koma can duk ta fige kamar mahaukaciya.
    Bakin kofar dakin Fahad din ta koma ta zauna tana kuka.

    Shikuwa yana kwanciya bacci ya daukesa dan yana bukatar hutawa dan gobe ko office baya tuannin zai ita fita.
 
   Nan tayi kwanciyar tah har aka kira sallar asbah.

   Shima kansa ya makara koda ya farka an idar da sallar dan haka toilet ya shiga yayi alwalar sa ya fito yayi  sannan ya koma ya kwanta dan bemasan Salma na kofar dakinsabah.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
  Yau ya kama Friday dan haka su Safiya yaune ranar dinner gida sai farin cikin dan Ango sai faman ruwan Naira yake musu su kuma sunata faman jin ddi.
    Amarya ansha gyara sai faman kanshi take ta kara kyau da ita gwanin sha'awa sai hidima take ita da kawayanta.
    Amma har yanzu cikin zuciyar ta batajin ddin rashin yr uwarta.
Ko da yaushe itama tana fatan ta dawo garesu duk da bata kaunarta.
 

    Shaheeda itama har yanzu kullum cikin kewar yr uwarta take dan bata da wani sauran walwala.saboda Sapna CE kawai farin cikinta dan har rashin lafiya tayi.
   Yqnxuma tana kwance kan kujera tana bacci duk ta rame kamar ba itaba gashi batasan cin Aunty Ummi CE kawai ke iya lallabata shiyasa yace da dan asabe in zata koma da ita zata tafi.
    Haka su rahama suma basa da wani sauran walwala dan har kwallah take inta tuna da Sapna.
    Husnah ma bata da lafiya dan ta fada sosai saboda tana kaunar kawar tata kullum fatanta Allah ya dawo musu da Sapna garesu.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
     ^~^~^~^~[ 11:30pm ] ^~^~^
  Sai lokacin Fahad ya fito daga dakinsa cikin shadda milk yayi kyau sosai ya saka hula da agogo sai faman kamshi yake zubawa.
    Da alama masallaci zai tafi koda ya fito bega salma awajanba.
Dama kuma besan da zamanta anan bah.
    Fita yayi ya shiga motarsa yabar gidan.

    Tana tsaye tana kallansa ta window harya fice daga gidan.
  Murmushi tayi tare da fadin "zaka dawo ka same ni"
   Sannan ta bar wajan.


Shikuwa masallaci ya nufa danyin sallar juma'a.
   Bayan an idar gidan su ya nufa.
   Koda ya shiga yayi parking motarsa,bayan sun gama gaisawa da masu aikin gidan ya kuma yi musu alkahari kamar yanda ya saba.
 Sannan ya shiga gidan .

    Da sallamarsa ya shiga falon babu kowa acikin falon.dan haka ya nufi kitchen dan kamar yaji muryar mummy tacan.
   Da sallama ya shiga,
 Zama yayi kan daya daga cikin Stoll dake ajje a gurin.
   Bayan ta amsa masa sallamarsa.sannan suka gaisa.
   Nan take tambayarsa ya iyalinsa.
   Nan ya gaya mata lafiya qlau suke.

    "Mummy ya za'ayi me kike hada manane yinwafa nakeji"
    "Dama aikinka kenan acicici kawai"
   Dariya yayi tare da shafa sajansa daya kwanta yayi kyau yace"haba mum nidin ne acicici?"
    "Eh kaifah ai baranar da zakazo gidannan bakaci abincibah"
  Shide Murmushi kawai yake sannan yace "nide a taimaka min kar yinwa ta sace ni"
  "Kaide ka Sani kana da matarka amma ace kullum kqna zama da yinwa ko ita me takeci a gidan oho"
 Zai yi magana wayrshi tayi kara.
   Fitovda ita yayi tare da gadawa.
  Bayan sun gaisa da nurse din take sanar masa cewa patient din ta farka.
  Nan ya sanr  da ita da yana zuwa..
   Mum CE ta juyo tana kallansa dan duk taji abinda nurse din ta fada.


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
 01 Amal fan's club 💅🏻 🌷



Written by Zeenaseer 😘
[24/3 23:24] Hussaina: ©EXQUISITE ONLINE WRITERS
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
                👑👑
                   🌳
        MARAICHI❣
               NA
  Zainab Naseer Sarki
      (Zeenaseer😘)


4⃣4⃣

      Tnkuuuu so much fr d Lov,support nd care my Cwt Kanwa 🎯hussaina Nasir Ubandiya🎯 Nagode sosai Allah bar zumunci.dis page goes to u my dear😘😘


⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜

•••••••Da sallama Fahad ya turo kofar dakin tare da shigowa.
    Mum ce ta amsa sallamar tashi tare da fadin "kadawo kenan?
    " eh" kawai yace tare da mika mata ledar dake hannunsa sannan yace "Nizan huce tunda naga kamar ba yanzu zaki tafi bah,inyaso inkin gama saiki kirani"
 Yana kaiwa nan ya juya ya fice da cikin dakin tare da janyo kofar dakin.
   Binshi tayi da kallo harya fice daga cikin dakin.
  Murmushi tayi tare da fude ledar.
   Riga da wandone irin na Pakistan masu dogon hannu da Vail dinsu,wandon red hakama Vail din,ita kuma rigar farace anyi mata ado da red kayan sanyi kyau sosai.
   Mikewa tayi tare da karasowa kusa da ita sosai sannan ta kuma shafa sumar kanta tare da fadin "em mata tashi ki saka kayan wannan ki cire na jikinki kinga sun bace".
   Ahankali ta mike zaune tare da taimakon mummy.
Har bakin kofar toilet din mummy ta rakata dan tana mugun jin tausayinta,sannan ta mika mata kayan.
    Ansa tayi tana kallan mummyn itama ta sakar mata Murmushi dan San matar ya shiga zuciyar ta.
    Tana shiga ta hau sanya  kayan.

Ita kuwa Mummy komawa tayi kan kujera ta zauna.

   Bayan lokuta kadan Sapna ta fito daga toilet din.mummy dake zaune ta fita da kallo dan kayan sunyi mata kyau sosai kamar ba Indian sunyi mata daidai kuma kamar yasan size dinta.
    Cikin tafiyarta me tsari ta karaso kan gadan ta zauna tare da sunkuyar da kanta tana wasa da yn yatsunta.
      "Ko zakici abincin na zuba miki? Mummy tayi mata wannan tambayar.
    Kai ta gya mata batare da tayi magana bah.
   Mikewa Mum din tayi ta zuba mata sannan ta mika mata.
    Amma ita ko kadan batajin yinwa kawaide ta ce " eh" ne dan taga mum din ta damu da hakan.
   Ahankali ta sanya cokalin ta fara ya mutsa abincin tana ci kadan kadan.
   Itama mum din sai kallanta take dan komai na yarinyar burgeta yake gata da hankali da nutsuwa.
   "Menene sunan ki yn mata?
   Ahankali ta sauke cokalin kanta a sunkuye tace " Sapna"
   "Allah Sarki Sapna sannu kinji"
   "Toh " tace da ita sannan ta Ajje abincin tare da fadin "nakoshi".
   " toh sannu ai kinmaci da yawa ba laifi"
   Ruwa ta janyo tasha sannan ta mike tare da fadin " zanyi sallah"
    "Toh maza kiyo alwala sai kixo kiyi"
   Mikewa tayi ta koma toilet din tayi alwala sannan ta fito ta tada sallah.



Har bayan sallar magrib mummy tana asibiti wajan Sapna har lokacin bata da shirin tafiya gida.
    Zaman da sukayi nadan wannan tym din Sapna taji ddin hakan kasancewar mummy nasanta kuma tana kula da ita.
   Shiyasa ta saki jiki da ita har suke er hira.

   Dayake ta sanar da Dad din Fahad duk abunda yake faruwa kuma shima ya tausaya mata sosai sannan yace tayi mata sannu kafin yaxo.

    Bayan sun idar da sallar ishsha suna zaune suna dan hira likita ta shigo ta kuma duba jikin Sapna ta bata wasu magungunan.
    Bayan ta gama duk abinda ya kamata ta kuma shaidawa mummy "zasu ita tafiya an basu sallama Allah ya kara sauki"
    Sosai Mummy tayi mata godiya sannan suka fara shirin tafiya.


   Yana kwance acikin dakinsa dan yau kusan a gida ya yini dan yana bukatar Hutu.
    Wayar shice tayi kara,hannu ya sanya ya janyota tare da daga da sallama.
   "Kqna ina kuma tunda ka tafi baka dawo bah?
   " amm wallahi ina gida ne"
  "Yayi maka kyau saika  zo ka daukemu dan sun bamu sallama"
   "Tqmm" kawai yace tare da kashe wayar sannan ya mike badan yasoba ya dauki key dinsa ya fito daga dakin.

Ahankali yake tafiya harya fito kofar falon inda zai fita waje.
   "Dakata Fahad" ta fada tare da tasowa daga kan kujerar da take a zaune.
   Cak! Ya tsaya tare da juyowa ya kalleta dan baiyi tsammanin tana cikin falonbah.
    "Ina kuma zaka da wannan tsohun daran? Ta jefo mai wannan tambayar tare da matsowa jikinsa har suna iya jin numfashin juna.
   Shiru yayi yana kallan ta yama rasa abunda zaice da ita.
   " meyasa vaka San farin cikina,kuma bakasan mu rinka zaman lafiya?
    Tana magana tana shafamai huya da hannunta tare da shinshinamai huya.
   Rufe idanunsa yayi tare da janye hannunta daya daga jikinta.
 Cikin wata kasa lalliyar murya yace da ita "ina zuwa yanzu zan dawo mu.....
   Batare da ya karashe maganarba ta sanya bakinta cikin nasa.
   Key din hannunsa ya sake tare da sa hannun nasa ya dafe bayanta dashi.
   Tuni ya manta da kiran da mummy ke masa ya dauketa cak daga falon zuwa dakinta.


  ^~^~^~^~11pm Suna jiranshi amma har lokacin be zoba,takurashi amma harta faji hakan ya sanya ranta ya baci.
   Itade Sapna tana zaune tana kallan yanda mum keta faman kiran waya amma anki dagawa sai faman tsaki take.
   Bakinta ta tabe tare da fadin"Allah sama yaki zuwa dan bani da bukatar ganinsa"

    Drivern ta ta kira dan yazo ya dauketa.Dama tun dazu taki iransane tasan yana cikin iyalinsa bata san  takuramai.
   Bayan ya dagane ta sanar masa da bukatar ta.

   Baidau wani tym me tsayiba ya karo asibitin nan suka fita suka shiga motar sai gida kuma.

   Bayan sun shigo gidan ne ta anje kayan cikin kitchen sannan ta kama hannun Sapna zuwa upstairs.
   Wani daki ta bude me kyau ga yalwa komai akwai aciki harda toilet.
   Nan ta shaida mata da ta zauna aciki koma ga toilet nan intana da bukatar canjin kaya zata iya.
   Taji ddi sosai sannan tayi mata godiya tare da shiga cikin dakin.
   Itama mummy barin wajan tayi.

   Sai faman kallan dakin take komai ya burgeta gwanin ban sha'awa, gashi ba datti komai a tsare.
    Fadawa tayi kan gadon tare da lumshe idanunta.
   Shaheeda CE ta fado mata arai."Allah Sarki ta furta ,Allah ne kadai yasan irin halin da zata shiga na rashin ganina"
    Tabbas tana bukatar ta koma gida dan ganin yar uwarta kuma tana san zama anan dan nemo Dagin mahaifiyarta da kuma ita kanta mamantasu.

    Wata zuciyarce tace da ita " Sapna kin Riga kinsan inda yn uwanki suke,yanzu vaki da zavin daya rage ki tashi tsaye dan nemo mamakin da yn uwanta kina bukatarsu,sune farin cikin ki"
   Toh "amma kuma ya zatayi da soyayar Kamal dake neman aa tah.

  Gaba daya ta shiga cikin rudani burinta tayi karatu me nisa tazama wata a fadin duniyarnan amma mundin ta koma gida ya Abba zai iya aura mata Wanda yaga Dama haka rayuwarta zata kare cikin bauta haka zata kare kenan.
    Dole ta zauna a bauchi ta samu ilimi me yawa kuma ta nemo mamanta.


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fan's club 💅🏻 🌷


Written by Zeenaseer😘
[24/3 23:24] Hussaina: ©EXQUISITE ONLINE WRITERS
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
       MARAICHI❣
              NA
  Zainab Naseer Sarki
     (Zeenaseer😘)


4⃣5⃣


•••••••••••Da wannan tunanin ta mike ta nufi toilet alwala ta kuma daurowa ta bude wardrobe ta dauko sallaya da hijab sannan ta tayar da sallah nafila dan neman kariya da nasara wajan Allah.
    Ta jima kan sallaya tana sallah sannan ta mike ta canza kaya zuwa doguwar Riga marar nauyi sannan tayi addu'a ta kwanta.

    Kiran sallar asbah a kunnan ta,tanaji ta mike tayo alwala sannan ta tada sallar.bayanta idar zama tayi tana addu'a kamar yanda ta saba har gari ya fara haske sannan ta koma gado dan baccin be isheta bah.
 
^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^
   Sai bayan yayi sallar asbah ya dawo dakinsa sannan ya tuna da barin mummy da yayi can asibiti..
   Hankalinsane ya tashi dan yasan be kautabah.
   Tunanin kiranta yayi sai kuma ya fasa tare da fadin sai de zuwa anjima zaije dan bada hakuri.


     Salma kuwa ganin kwana biyu bata gaban me gidan nata ,ya sanya zata gyara halayanta dan ya kara Santa da kuma kaunarta harma ya dena tunanin wata acan waje.
   Itama bayan tayi sallah bata koma bcci bah.
  Aiki ta shiga yi,ta gyara ko ina sannan ta nufi kitchen dan hada masa breakfast.
    Saida ta gama komai sannan ta koma dakinta dan lokacin 10am ta kusa.
   Wanka ta tsala sannan tayi kwalliya tayi kyau sosai kamar ba itaba.
   Dakinsa ta nufa tana faman rangwada.

^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^
  ^~^~^~ 10am lokacinne Sapna ta tashi daga bacci,bayan tayi wanka ta zauna gaban mudubi ta danyi light makeup sannan ta sanya Riga da skirt na atamfa tayi kyau sosai dande tadan rame,gyara gashinta tayi ta feshe jikinta da turare.
   Ahankali ta mike ta nufi bakin window tana kallan yanada garin yayi kyau,ga kuma bishiyo da suke faman kadawa abun saiya burgeta.
   Tabbas hutuma wani Abu ne,hankalinta harya dan kwanta amma da yanzu tana can tana faman uban aiki.
  Murmushi ta kuma yi tare da rufe labulan gurin ta juya ta fice daga cikin daki.


^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^
^~^~^~^~ 10am  shine daidai lokacin da ake kaima Sapna abinci cikin rijiya.
   Bayan ya gama hada abunda zai kai mata ya nufi dakin ya bude.
   Sakin ledar hannunsa yayi tare da kara sowa wajan da yaga abin sink din ga kuma jini agurin.
  Daga kansa ya kuma yi sannan yaga gurin da aka sauke glass din.
  Da sauri ya kuma komawa wajan rijiyar ya leka.
   Gaba daya ya rude kamar mahaukaci.
  Daga cikin dakin ya fito sannan ya zagaya baya dan ganin inda Sapna ta sauka.
   Gurin yabi da kallo tare da ci gaba dabin hanyar dayaga da alamun jini har bakin titi.
   Wani wawan ihu ya zuba tare da fadin "tafdi Jan lallai yarinyar nan ba karamin kokari tayi bah"
   Gaba daya mamaki ya kamasa wayarsa ya fito daga cikin aljihunsa dan ya sanar dasu  bash da huri dan asan abinyi.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
   Yaune ya kama daurin auran Kamal da Safiya.
  Kofar gidan ya cika da jama'a Ango sai faman washe baki yake dan murna.
   Mutane sai hada  hada ake.duk rabin mutanan gurin abokan Kamal ne in iska sai kuma dangin Umma da sauran jama'ar unguwa.
    Daurin auran yayi jama'a sosai.
 
   Wayar bash ce tayi kara.
   Hannun sa ya sanya cikin aljihu tare da dauko wayar.
   Jama'ar dake wajansa ya dagama hannu tare da komawa gefe.

   "Ya akayine ka kirani da wannan tym din?
  " Wallahi ansamu matsala ba karamabah kuwa"
    "Meyeshi ka gayamin pls kasan bani da lokaci yanxu kawai abun ya dace ayi inyaso da anjima mayi mafana"
   "Kaga wannan fah ba maganar anjima bace Sapna ce ta gudu kuma da alama tun jiya ta gudu"
  "Whaaat!" Ya fada tare da cire hular kansa dan danan gumi ya fara keto masa.kana ganinsa kaga marar gaskiya sai faman kallan mutane yake yana basarwa.
    "Haba Habu,ya zakayi mana haka shekara nawa muna aiki ba'a taba samun matsalaba sai yau,kaga dan Allah kasan abunyi pls kafin Kamal ya Sani kasan dagani har kai babu Wanda zaiji ddi"
   " Babu damuwa insha Allah za'a san abinyi"
   Sannan sukayi sallama ya kashe wayar.
Gaba daya jikinsa yayi sanyi dan be tafa tunanin hakabah.

    Haka ya koma cin jama'a akaita hidima har lokacin daurin auran yayi 10:30am haka aura kowa kuma ya shaidah.
    Shide haka aka watse hankalinshi atashe.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
   Ahankali ta tura kofar dakin nasa.
  Yana tsaye kaban mudubi ya gama shiryawa yana fesa turare.
   Ahankali ta tako tare da rungumeshi ta baya,kusa da kunnan sa ta matsa tare da fadin "Morning my Prince" da Murmushi dauke a fuskarta.
    Shima Murmushi yayi ya juyo da ita gabansa tare da kama kugunta shima yace mata "Morning cwthrt"
     Rungumeshi tayi tare da fadin"kayi kyau sosai"
  "Hmmm! Ai ban kaikiba my Preety wyf"
   Murmushi ta kumayi"muje na hada maka breakfast "ta dago da kanta tana kallansa.
   Shima kallan nata yake sannan ya manna mata peck a hanci tare da Jan hannun ta suka fice daga dakin.

^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^
    Ahankali take sakowa daga steps din benan tana kallan tsarin gidan harta sakko kasa.
   Bataga kowa cikin falon bah, dan haka tsayawa tayi tana kalle kalle.
   Can taji karan kwanika a wajan corridor. Hanyar tabi dan tana tsammanin kitchen ne.
   Tana karasa kuwa mummy ta gani tana fitowa dauke da flask a hannunta.
   Matsawa tayi tare da durkusawa ta gaidata.
   Murmushi tayi itama ta amsa ganin yanda Sapna ta saki jikinta harta sanya kayan jikinta.
    Saida ta kuma dubata sannan tace" ta mike ta zauna kan dinning danyin breakfast.
      zama tayi tana wasa da yatsunta kafin Mummy tayi serving dinta.
    "Aa Sapna ki zuba abinda zakici mana,maza ki zuba kici"
   Murmushi itama tayi sannan ta mike tana dan jin kunya ta zuba abinda zataci ta farci,itama mummy ta zauna danyin breakfast din.
   Ba laifi tadnci abinci kuma ta saki jikinta sosai da mum din hakan ba karamin ddi yayimatabah.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
 Shide Bash tunda aka sanar masa da guduwar da Sapna tayi hankalinsa ya tashi gashi kuma ya kasa gayama kamal din..
 
   Bayan sun dawo daga wajan daurin auran suna zaune a falo suna hira amma Bash hankalinshi baya jikinsa yana tsaoran karta tona musu asiri.
 
   "Bash wai lafiyarka qlau kuwa duk naga ka canza?.
   Wayancewa yayi tare da yin Murmushin dole" ya! Banajin ddine fah"
  "Abeg don lay to me,ur hiding sumthng yane?
   Shiru yayi tare da jingina kansa jikin kujera idansa a rufe.
   Murmushi Kamal yayi tare da zuba wine cikin cup zai sha.
   " me yasa kake tsoran gayamin Sapna ta gudu"ya karshe maganar tare da sanya cup din a bakinsa.
   Da Saudi ya dago daga kwancan da yake ya zaro Ido yana kallnsa cikin mamaki😳




😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fan's club 💅🏻 🌷



Written by Zeenaseer😘
[24/3 23:24] Hussaina: ©EXQUISITE ONLINE WRITERS
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
       MARAICHI❣
               NA
  Zainab Naseer Sarki
      (Zeenaseer😘)



4⃣6⃣


•••••••••Ajje cup din yayi yana Murmushi "kana mamakin yanda akai  nasan Sapna ta gudu ko?
   Da sauri ya shiga girgirza kai alamun eh!
   " Bash kenan Bara kaji na fada maka na huce duk inda kake tunani kuma ina me tambatar maka duk lokacin da naga Dama zanje na dauko Sapna daga gidan su Fahad.
  Sabo da haka ka kula"
 Ya karashe maganar tare da mikewa yabar falon.
  Shikuwa sakin baki dan tsabar mamaki "kenan ma har yasan sunan gidan su Wanda take,Dankari! Kace akwai tashin hankali agaba"
   Mikewa yayi da sauri ya sanya hularshi dan yau za'a kawo wa  kamal Amaryarsa.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
   Zaune suke saman dining sunacin abinci suna hira kamar ba sune ke faman fadaba koda yaushe.
   Cikin salon Jan hankali take komai nata, cikin wata murya ta salan yaudara tace da Fahad "baby ni kuwa waye bashi da lafiya jiya naga ka damu da kaje har kana kokarin bada jini?
    Bayan ya kai lomar abinci bakinsa ya cinye sannan ya ajje spoon din,Murmushi ya saki da yake kara masa kyau .
   Nan ya sanar da ita komai dangane da Sapna.
  Nunawa tayi bata damuba harda yimata addu'a neman sauki.
  Amma cikin zuciyar ta mugun tafasa take tanajin ko yanzu aka bara bindiga zata ita kashe tah.
  Ko ba komai yayi mugun jin ddin sauyin da aka samu a gidansa.
   Dan haka bayan sun gama breakfast din ya sanar mata cewa zaije gida ya kuma duba me jiki,kuma yasan mummy tana nemansa.
   Munawa tayi zata bishi itama ta duba Sapna.
   Ita kuwa tayi hakanne dan taga wace wannan dahar ta samu nasanar amfani da jinin mijinta.

Bayan ta gama abinda zatayi sannan suka fito dan tafiya gidan nasu.

^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^
   Bayan sun gama breakfast din Sapna ta takura saita yima mummy gyaran kitchen, badan tasoba ta rabu da ita.
   Aikuwa ta gyara mata ko ina duk da babu dirty dan Mummy mace ce mai tsafta sosai.
   Bayan ta gamane ta dawo falo kan kujera suka zauna suna dan taba hira suna kallan TV.

   Sallama da sukaji ce ta sanyasu kallan kofa dan ganin masu shigowa duk da mum tasan muryar Fahad CE.
   Karasa shigowa sukayi tare da zama kan kujera.
   Cikin sanyin jiki Salma ta gaida mum dan tunda rayi ido biyu da Sapna gabanta ke fadu,dan ko ba'a fada bah tasan itace,lallai akwai aiki agabanta ba karami bah.mundin yana ganin yarinyar nan wata rana dole ya nuna yana santa.

    Cikin sakin fuska mum ta amsa gaisuwar tasu.
   Cikin muryarta me ddin da sanyi ta gaida su Fahad.
   Duk kallan ta sukayi sannan suka amsa.
  Ita kuwa Salma sai kallan Fahad take dan taga irin kallan da yakema Sapna.
   Shikuwa Fahad kallan ta yake kamar ba itaba yaga ta kara kyau tayi fes.
  Dauke kansa yayi sukaci gaba da hira da mum.
   Itama tunda ta gaidasu suka yimata ya jiki ta dauke kanta daga garesu taci gaba da kallan TV abunta.

  Salma ta kasa sukuni gaba daya dan gani take kamar Fahad san Sapna yake da irin yanayin kallan da yake mata.
   Gaba daya hankalinta ya tashi har wani gumi take dan masifah.

   Suna nan zaune su mum sunata hirar su ita da danta har aka kira azzahar.
   Nan ya mike dan zuwa masallaci.
   Itama Sapna mikewa tayi ta nufi dakin tah.
  Mum kuma taja Salma dan taje dakinta tayi sallah.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
  Yau ake yini gidan su Amarya Safiya sai faman shagali ake gida ya cika makil,wasu na zuwa wasu na tafiya.
   Kowa da abunda ya dameshi,wasu na hira,wasu cin abinci,wasu kuma na aiki.

   Har part din Rahma cike yake jama'a.
  Shaheeda kuwa na kwance kan gadan Rahma tana bacci duk ta rame,bata da aiki sai bacci gashi kullum da daddare sai tayi zazzabi danma Aunty Ummie na kula da ita sosai.

  Bayan sallar magriba kofar gidan ya ciki da motocin kai Amarya. Mutane sai shiga ake kai Amarya.
   Ita kuwa tana daki tana faman kukan rabuwa da gida da yana uwanta.
  Sai nasiya manya ke mata haka aka fito da Ita aka sanyata cikin mota sai gidan Kamal.

   Mutane na isa me gadi Dama yasan da zuwansu haka sukayita shiga har motar amaryar ta iso.
   Gidan da suke zaune shida bash nan aka mata Jere a dayan part din.
  Yayi kawai sosai da yake gidan ba lefi yana da girma ko ina an tsara shi yanda ya kamata.

Haka aka yi santin gidan har kuma lokacin watsewar jama'a yayi sannan akayima Amarya sallama suka tafi aka barta ita kadai.

^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^
    Shikuwa Kamal yana can club abokansa sun hada masa party sai faman shaye shaye suke suna rawa da emmeta.
   Babu abunda ke tashi awajan banda hayakin wiwi da kida.
Mata da maza en iska sai faman rawa ake ana watsewa(ALLAH UBANGIJI YA SHIRYE MU SHIRIN ADDININ MUSLINCI AMEEN🙏🏻)


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
   Bayan Sapna ta idar da sallar ta sauko kasa bataga kowaba kuma batasan dakin mum dinba.
  Saita zauna akan kujera rana jiran fitowarsu dan batasan zama ita kadai.
  Fahad ne ya shigo da sallama tare da zama kan kujera.
   Batare da takalli inda yakebah ta amsa mai sallamar tare daci gaba da abunda takeyi.
   Shima din ba damuwa yayi da itaba dan haka ya shiga neman layin Salma danya sanar mata zai je ya dawo inyaso saiya dauketa su tafi.
  Bayan ta dauka ya sanar da sakonsa mikewa tayi dan tafiya.
  Ahankali Sapna ta furta Nagode batare da ta kuma cewa komaibah ta mike tabar wajan.
    Shikuwa inta yayi da kallo Santa raina masa hankali,sai yanzuma zatace masa ta gode.
   Itama Salma bakin cikine ya kamata ganin yanda Fahad yake kallan wannan kwailar yarinyar har wani yanga take mai.😛



😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fan's club 💅🏻 🌷


Written by Zeenaseer😘
[24/3 23:24] Hussaina: ©EXQUISITE ONLINE WRITERS
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
       MARAICHI❣
              NA
   Zainab Naseer Sarki
       (Zeenaseer😘)



4⃣7⃣


•••••••••Kamar zatayi kuka dan takaicinsu.
Da ker ta ita karasa saukowa daga kan steps din benan harta karaso kusa dashi har lokacin yana tsaye be tafi bah.
   Muryar ta na rawa tace dashi"me kuma kakeyi anan wajan Fahad?
   Batare da ya bata amsaba yace saina dawo kawai.
Juyawa yayi ya fita daga cikin falon tare da turo kofar dan shima ranshi ya bace dan yana ganin kamar Sapna har wani Ji dakai take.
  Tsaki yaja ya shige cikin motarsa "toh tama ja ajinta mana,meye nawa aciki"
   Ficewa yayi daga gidan ya nufi cikin gari.


    Bayan mum ta dauko tare da Sapna suka shiga kitchen suka dafa launch.
   Ita kuma Salma tana falo dan ita yanzu ko ganin Sapna bata kaunar yi.
   Saida suka gama komai sannan suka kirata dan tazo suci.
   Cewa tayi ita ba'a lokacin zatacibah sai zuwa anjima.
   Nan suka zauna sukaci suka koshi suna hirar su harda dariya.
   Ita kuwa Ji take kamar ta rufesu da duka.

  Hakade ta yini babu wani walwala atare da ita.
  Ita kuwa Sapna Ji take kamar agida take dan sun saba da Mum sosai.


Bayan sallar magrib Fahad ya shigo tare da Dad dinsa.
  A falo suka zauna suna hira har mum ta fito daga daki dan zuba musu abinci.
   Saida kowa yaci ya koshi banda Sapna da ta tafi daki dan ita kunyar Fahad da haushinsa takeji shiyasa bata sakewa agabansa.
   Sai bayan su fahad sun tafi sannan mum ta kirata.
   Bayan ta gama cin abincin ta.
  Mum ta kirata falo.
   Tana zuwa suka gaisa da Dad shima yana da fara'a kuma ya qmsheta hannu bibiyo kuma ya tausaya mata da hadarin daya sameta.

   Suna zaune saman kujera ita kuma tana kasa ta sunkuyar da kanta.
  Mum tace ta da Sapna "kamar yanda yanda muka qnsheki tsakani da Allah kuma muke da fatan rikeki tsakani da Allah inhar kina da bukatar hakan dan Allah kada ki buye mana komai ki fada mana abunda ya raba ki da iyayanki?
   Murmushi tayi nan danna kwallah ta cika mata idanunta sannan tace "Mummy koda baki hada ni da Allah ba,kuma ko mutun jahiline shi ayanda kuke da san mutane kuke darajasu baku cancanta a gaya muku karyaba.
  Nan ta fara basu labarinta tundaga inda tasan tana da wayo har zuwa ranar da Fahad ya taimaka mata.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
  ^~^~^~11:53pm har lokacin Kamal be shigo gidan ba.
   Safiya harta gaji da lullube lullubenta ta tashi tayi sallah ta canza kaya amma shiru babu shi babu labarinsa.
   Abunda ya bata tsoro kenan.
Mikewa tayi ahankali ta fito falo tana rabe rabe kamar wata munafuka.
   Harta fito tsakiyar falon.
Ko ina da hasken wuta.
Nan ta kama kallan jernta komai ya burgeta kuma an tsarashi yanda ya kamata.

   Tana nannzaune taji karan bude gate da sauri ta Mike tsaye tana kallan kofa.
    Bayan kamar 2mins taji an turo kofar dakin.
   Wata budurwace Wanda shekarunta bazasu haura 22 ta shigo rike da Kamal yana tangadi kamar zai fadi.
   Tasa wasu kaya masu nuna tsiraici sai wani yanga take.
Bash yana bayansu yana nuna mata dakin dazata kaishi.
 
   Gaba daya Safiya tama rasa awace duniyar take mafarkine ko gaske.
   fadawa tayi kan kujera batare data saniba.
   Hawayene ya shiga sauko mata wani nabin wani.
   "Wannan wani irin iskancine haka,Dama Kamal dan iskane,kuma dan shaye shaye?
   Wannan tambayar da takeyiwa kanta kenan Wanda bata da amsarsu kuma bata  saniba,saide abunda idanta ya gane mata kenan.

   Da sauri ta kuma dagowa da idanunta da sukayi jajar lokaci daya.
   Bash ne da wannan budurwar suka fito daga dakin.
   Yana rike da ita har sukai bakin kofa zasu fita sai budurwar ta juya tare da kallan Safiya.
   Kallan bash tayi tare da nuna Safiya, daga mata kai yayi yana Murmushi alamun eh.
   Da Sauri ta karaso inda Safiya take tare da fadin "Amaryarmu oyoyo ta rungumeta".
   Itade tana tsaye kamar wata gunki.
   Kiss ta manna mata a kumatu tare da fadin " bye Amarya dare tayi sai gobe zamu kawo miki ziyara pls kiyi hakuri"
   Sannan ta juaya suka fice.
  Komawa tayi ta zauna tare da kuma fashewa da wani saban kukan.
   "Shikenan na cuci rayuwata,na cuci kaina,Ashe Kamal ba alheri bane a gareni.na kuka yau dari Sapna yanzu ko tana ina baiwar Allah,kuka sosai taci gaba dayi tana tunawa kanata asiri.
   Yanda taga rana haka taga dare dan wani Abu me suna bacci ko tasusa da idanta be huce bah.
   Banda kuka babu abunda take idanta duk sun kumbura gashi kanta sai faman ciwo yake.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
   Koda su Salma suka koma gida gaba daya bata da walwala.
   Fahad ne daya gane hakan ya tambayeta.
   Memakun ta bashi amsa saita fashe da kuka.
Hankalinsane ya tashi ganin yanda take kukan.
   Da ker ya samu ya lallaaheta.
Nan ta tambayeshi ko yana san Sapna.
    Dariyama ta bashi.
 Nan yayi ta mata dariya.
Dukan wasa ta kaimasa tana kwallah.
Rungumeta yayi tare da fadin" kinga ki kwantar da hankalinki ni basanta nakeba,asalima yarinyar bata yimin bah.
Dan haka kibar damun kanki,kodama aure zan kara na rasa matar aure sai wannan yarinyar ballema daga ke ba kari"
    Kara makaleshi tayi tana dariya dan jin ddin yanda ya mata bayanin komai kuma tasan da gaske yake.
    Kuma ta dau alkawarin yimasa biyayya mundin bazai yimata kishiyabah.

^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^
   Daga Mummy har Dad babu Wanda be tausayama rayuwar Sapna bah.
   Dan Mum har kwallah ta zubar mata.
   Nan ta taso ta rungumeta tana share mata hawayan nata.
  "Ya isa haka Sapna insha Allah zaki zauna awajanmu kamar yanda kike bukata,zamuyi miki duk kan abunda iyaye na gari ya kamata suyima yaransu,ina me tambatar miki za'a yi alfahari da ke da zuria'arki insha Allah.
   Allah ubngiji ya albarkaci rayuwarki"
   "Ameen" ta furta.
  Sannan mum tace ta koma dakinta saida safe.

Nan suka zauna ita da Dad suna kara jinjina al'amarin dan Umma ta cika azzalima.
   Nan Dad yace zai neman mata makarantar da zata kara shiga SS3 tayi exam dinta dan ci gaba da karatunta kuma da gurinnemu mamanta da danginta.
    Mummy taji ddi sosai kuma tayi masa godiya shima.



😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fan's club 💅🏻 🌷


Written by Zeenaseer😘
[24/3 23:25] Hussaina: ©EXQUISITE ONLINE WRITERS                      🌳🌳        ⚜      🌳🌳🌳                             🌳
               👑👑
                  🌳
       MARAICHI❣
            NA
  Zainab Naseer Sarki
       (Zeenaseer😘)
   

4⃣8⃣

👰🏻👰🏻👰🏻👰🏻👰🏻👰🏻👰🏻👰🏻👰🏻👰🏻
                 ❤                                We are cute duaghters,
we are sweet sisters,
we are lovely lovers,
we are darling wives,
we are adorable mothers,
we are source of strength,
we are WOMEN!
            ❤❣❤
 I'm wishing you a days which is as bright as Ur eyes and every one around U 2B AS generous as Ur heart.
    I just wrote dis,just to make U guys happy nd to make u happier.
   We are d best ever nd Ur always proud of our self cux we deserve that.
  May god protect us,
May sadness 4get us,
May goodness surround us,
May happiness be around us,
And may god always bless us.
   Rwwly lovs you guys to d moon nd bck and my best wishes to you JANNATUL FIRDOUS.
   I promise to be always remember u nd prayed for u guys.pls nd pls don't 4get I always need Ur prayers 🙏🏻
             ❣❤❣
I DEDICATED DIS PAGE TO ALL MUSLIM WOMEN🌬
👰🏻👰🏻👰🏻👰🏻👰🏻👰🏻👰🏻👰🏻👰🏻👰🏻




⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
••••••••• Kwana Safiya tayi batayi bacci ba sabo da abunda idanta ya gane mata daran jiya.
   Kuka tasha sosai dan fuskarta farta kumbura.
   Mikewa tayi daga kan kujerar da take tun daran jiyan.
Toilet ta nufa ahankali take tafiyar kamar kazar da kwai ya fashema aciki.
   Tunda ta shiga toilet din take kallan kanta jikin mirror toilet din.
Kwalbar freshener ta dauka tare da fasa mirror dashi.
   Ka tayi da baya ta jingina jikin bango tare da fashewa da wani saban kukan.
   Tabbas Kamal yqci amanar ta,daran jiya ya zame mata tamkar daran mutuwarta.
   Gaba daya mafarkin da take da kuma rayuwar da take tsarawa ita da mijinta yanzu babu ita.
   Kuka sosai takeyi babu me lallashinta.
Hada kanta tayi da gwiwa tare da zama cikin toilet din taci gaba da kukanta.

   Turo kofar toilet din yayi tare da tsayawa bakin kofa yana kallanta.
   Ahankali ta dago da jajayan idanunta da suka rune dan kuka ta saukesu akansa sannan ta maida kanta cikin cinyarta.
   Karasowa wajan yayi sanye yake da gajeran wando ba Riga ajikinsa.
   Ahankali ya durkusa tare da dago fuskarta yana kalo.
   Mikewa tsaye tayi da sauri tare da matsawa daga inda yake.
   Shima mikewar yayi tare da Binta.
  Tana ja da baya shima yana matsowa har suka kai jikin bago.
   Rufe idanta tayi tare da juyar da kanta gefe daya.
  Hannu ya sanya tare da goge mata hawayan dake bin kumatunta.
   Da sauri ta sanya hannunta ta ture nasa.
  Da dan yatsa ta nunasa Ido jajar yana fitar da ruwa murya na karkarwa tace dashi.
  "Kada ka kuskura ka kuma tabani da wannan kazamin hannun naka"
   Tana kaiwa nan ta fice daga toilet din.

Murmushi yayi tare da Binta.
   Zaune ya sameta cikin falo saman kujera ta rumtse idanunta.
   Karsowa yayi ya zauna kusa da ita.
   Mikewa tayi da niyar barmai wajan.
   Danko hannunta yayi tare da janta jikinsa.

Kan kirjinsa ta fada,Kwantar da ita kan kujera ya shiga yi.
Kuka itakuma take masa tare da kokarin kwace kanta.
   Bakinsa ya sanya cikin nata.
   Tun tana xillewa har jikinta ya saki ta kwanta kan kujerar.
  Tsawan lokaci suka dauka ahaka kafin ya saki bakinta ya rungumeta.
   "Pls kiyi hakuri wallahi sharrin shedanne insha Allah hakan bazata kara baruwaba pls my soul.
   Shiru tayi batare data rungumeshi ba,tana sauraran abunda yake fada.
  Sauran wahayan dake idantane ya gangaro,
Batasan lokacin data rungumeshi shi ajikintabah tana kukan.
   Murmushi ya kuyi tare da kara matseta ajikinsa.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
   Bayan ta tashi da safe tayi wankanta kamar yanda ta saba.
   Falon ta sauko ganin mummy bata nan yasanya shiga kitchen nan ma bata gantaba.
  Nan ta hau kokarin hada musu breakfast.
   Har tayi ta gama amma bata sauko bah.

Tana cikin jerawa a dinning ta sauko tare da fadin " a a a mezan gani karde abincin patient zamuci yau"
  Murmushi Sapna tayi tare da durkusa "mummy ina kwana"
 "Lafiya qlau Sapna kin tashi lafiya ya Karin saukin jikin"
  "Alhmdullh"
 "Masha Allah sannu da aiki"
  Itade kawai Murmushi take batare da tace komai bah.

  Zama sukayi sukayi breakfast dinsu,mum tana ta faman santin abincin Sapna.
  "Sapna irin want delicious haka ai saiki kwacemin Dad din ya dawo naki"
  Durkusar da kanta tayi tare da Murmushi dan jin kunyar da maganar mum ta fada.

  Suna cin abinci suna barkwanci har Dad ya sauko ya tarda su anan wajan.
  Shima kujera yaja ya zauna a daya daga cikin na dinning din.
Banyan sun gaisa da Sapna ta mike zata tafi.
"Ina kuma zaki je sapna ?
  Dad ya yi mata wannan tambayar lokacin da take kokarin barin wajan.
" amm ......hm dama zan baku gurine"ta fada kanta a kasa.
  "Gidanku" Dad ya fada "dawo ki zauna".
  Dago kanta tare da kallan Mum.
 Itama ita take kallan nuni ta mata alamun ta zauna.
  Komawa tayi ta zauna.amma ta kasa ci gaba da cin abincin.
  " Sapna "Dad ya kira sunan tah.
  " Naam" ta amsa tana wasa da Cokalin hannunta.
 "Ki saki jikinki ki daukemu kamar iyayan da suka haifeki kinji"
  Kanta ta gyada tare da fadin "eh".
   " masha Allah yanzu zakuje da Mum dinki ki zafi school din da kikesa kiyi jarabawanki,kuma zata kaiki kasuwa ki siyi duk abunda kike bukata"
   Kasa cewa komai tayi hawayn  daya digo ne Mum ta gane kuka take.
  "Sapna manah! Kukan na menene uhm"
  Ahankali ta taso daga kujerar da take ta karasa tare da rungume mum tare da fashewa da wani saban kukan tare da fadin "Nagode Allah ubangiji ya saka muku da gidan aljanna ya kara arziki da lafiya,Nago......"
  Bata karasa maganar ba Mum Ta toshi mata baki tare da fadin "kada na kuma jin kalmar godiya abakin nan"
Ta karashe maganar tare da jan en lips dinta dayasha lipstick.
   Murmushi tayi "amma Mum dame kikesan na saka muku?
  " Sapna kenan nasan duk abunda na nema awajanki babu tantama zan same shi,dan haka duk lokacin da bukatar ya tashi zan fada miki"
  "Nikuma nayi muku alkawarin dukkan abunda kuke bukata zan mukushi mundun be sabama shari'a bah"
   Shima Dad Murmushi yayi dan ya yaba da hankalinta"Allah ya albarkace ki"
  Shima ya fada.

Nan yayi musu sallama ya fita.
   Ita kuma Sapna ta kwashe kwanikan sai Murmushi take na far in ciki.


^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^
 "Dan Allah ka hakura da zuwa gidan mana pls"
   "Haba bby da raina da lafiya ta naki zuwa na gaida iyayena it can be possible bby,kema kinsan bazai yiyoba,just kawai kina nunawa as is dat u didn't truth me right"
  "No bahaka bane in muna tare wlh bnsan kayi nisa danine"
 "Ix OK! Kinga yau Sunday, ina gida mum zan dawo"
  Shiru tayi batace komaiba mikewa tayi daga jikinsa ta fice daga dakin tare da janyo kofar.
  Murmushi yayi tare da fadin"Salma rigima "
  Sannan a mike ya shiga toilet dan yin wanka yaje yayi sallar azhr.


  Ita kuwa duk tanayin hakanne dankar yaje yaga Sapna jitake kamar ta bishi.
  Dan gaba daya wannan yarinyar bata kwanta mata bah.


Bayan ya gama shirinsa ya saka farar shanda Riga da wando dinkin yayi mai kyau be saka hulaba agogo kawai ya saka da takalmi ya day key dinsa ya fita sai kanshi yake.
   Dakin Salma ya shiga itama daga wanka ta fito tana shafa mai.
  Kallo daya tayi mai sabo da kishi ganin yanda yayi kyau zai fita wata ta kalle mata shi.
   Har inda take ya karaso.
 Kiss ya manna mata a huya tare da fadin daya dawo.
  Binshi tayi da kallo harya fice daga dakin...




😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fan's club 💅🏻🌷


Written by Zeenaseer😘
[24/3 23:25] Hussaina: ©EXQUISITE ONLINE WRITERS
🌳🌳       ⚜        🌳🌳
🌳                              🌳
              👑👑
                🌳
     MARAICHI❣
              NA
 Zainab Naseer Sarki
      (Zeenaseer😘)



4⃣9⃣



•••••ONE WEEK LATER••••

       Sapna ta fara zuwa makaranta kuma Alhmdullh taji ddin makarantar sosai harta saba da wata Zee.dan halinsu yazo kusan daya kuma a guri daya suke zama.
    Haka duk abunda take bukata ta samu dan mum babu abunda bata yimata.
Har waya da laptop an shiya mata.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
   Karfe 11pm Kamal ya shigo cikin gida dan kwana biyu bai nuna mata wani hali marar kyau shiyasa suka saba dashi.
   Koda ya shigo falon bega kowa ba dan haka ya nufi dakinta.
   Kwance ya sameta kan gado kamar tana bacci amma idanta biyu.
  Har zai fita kuma saiya dawo.
  Ahankali ya fara hura mata iska cikin kunnan tah.
  Sannan taji lokacin shigowarsa shiya sa bata ji tsoro bah.
   "Safiya" ya kira sunan tah.
 Tashi zaune tayi ta mustsika idanu alamun bacci takeyi.
  "Harka dawo? Naga baka shigoba tun dazu shiya sa nadan kwanta"
   Wayar sace tayi kara.
Hannun sa ya zura cikin aljihu tare da daukota ya kara a kunnan sa.
   "Hello" ya fada dan yasan me kiran nasa.
 "Haba Kamal ya zakamin haka kasan na cemaka yaune birthday dina kuma kuma by 11:30pm za'a ynka cake kuma har yanzu baka zobah"
   Hannun shi ya Dora a goshi tare da fadin "pls am sorry wallahi na manta amma ganinan zuwa soon"
   Kallan shi kawai Safiya take bayan ya shigo yanzu kuma yace ze fita bayan tajima kamar da mace yake wayar.
   Cikin aljihunsa ya sanya wayr sannan ya kalleta da Murmushi "zan fita ba lallai na dawo yau ba maybe sai gobe"
   Kallan shi kawai take kamar zatayi kuka,she ix total speechless.
   Har yakai bakin kofa zai fita,da ker ta tattaro maganar ta sabo da wani bakin kishi daya tokare mata zuciyarta.
  "Kamaal" ta fada.
  Cak! Ya tsaya tare da juyowa yana kallanta alamun yana jiran abinda zata fada.
  "Kamal yanzu fa ka shigo gidan ina kuma Zak..."
   "Dakata" ya fada be barta ta karasa maganar bah.
   "Ni nake auranki koke ke aurena?,ina da right na zuwa duk inda naga Dama,dan haka kema zaki iya tafiya,ban hanakiba ga kofanan"
  Ya karashe maganar yana nuna mata kofar fita.
  Kwallar data ciko idantace ta zubo.
   Ko kallanta beyiba ya fice daga cikin dakin tare da janyo mata kofar.
    Fillonta ta janyo ta kwanta hawaye wani nabin wani.
 Waiyau ita namiji ke hulakantawa tabbas zata dau babban mataki akan Kamal, zata sanar da umman ta.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
   "Fahad pls kabar aikin office din nan inasan magana dakai"
  "Pls ki bari mana na,nakusan kara sawa pls bby"
   Ya karashe maganar yana kallanta.
  Kusa dashi ta dawo ta zauna tana jin haushi kamar zatayi kuka.
  Ture laptop din gefe yayi tare da juyowa yana fuskantar ta "fadi abunda kike san fadi"
  Murmushi ta danyi tare da fadin"amma Dama ina san naci gaba da aikinane pls tunda kaga yanzu babu wata matsala"
  Shiru yayi nadan lokaci kafin yace "amm pls baby kibar wannan maganar kissan aikin nan shine ke kawo mana matsala dan haka ki janye maganar in salaryn ne naca zanna baki duk mnth din pls"
  "Amma kasan yanda nakesan teacher kuma ni gaskiya zaman gida ya isheni"
  "Baby mata nawane suke zaune acikin gidan batare da aikin ba just su bawa mazajansu da yayansu kulawa ta musamma kibar maganar aikin nan banaso"
   Kallan shi take kamar ta fashe da kuka dan haushi.
"Amma ni gaskiya bazan ita zaman gidaba kullum babu kowa saini kadai"
  "Hmmm! Ke kika jama kanki,kince bakyasan yara,bakyasan jama'a toh yakuma kikesan nayi dake,kinga nafa gaji da abunda kike yimin Salma duk inda na bulla saikice banan ba kiyi yarda kike so"
   Juyawa yayi yaci gaba da abunda yakeyi.
  Kuka ta zauna tana mai kamar karamar yarinya.
   Banza yayi da ita harya gama jikinsa ya maida komai inda yake amma still kukan take.
   Toilet ya shiga yayi brush da alwala sannan ya dawo ya kwanta.
   Yana jinta,ya rabu da ita.
  Sam!  kukan ya tsaya masa cikin ransa dan bayasan jin kuka.
   Tasowa yayi enda take tare da rungumeta yana rarrashinta.
  Amma takiyin shirun.bakinsa ya hada da nata ya fara tsotsa dan Dama yana bukatar tah.
  Biye masa tayi,saida sukai tsawan lokaci sannan ya fara kokarin rabata da rigar jikinta.
  Hannutasa tare da tureshi ta mike tabar masa dakin.
   Ko motsawa beyiba daga inda yake,kawai rufe idansa yayi yana sauke ajjiyar zuciya dan abukace yake.
  Tsawan lokaci ya dauka sannan ya mike ya shiga toilet wanka yayi sannan ya fito yayi sallar nafila kana ya kwanta.


^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^
Sapna kuwa tana daki akwance kawai tunanin gida take,tayi shiru ita kadai abun tausayi.
   Mikewa tayi sanye take da kayan bacci Riga da wando farare tas,ta daure gashinta ta sako jelar gefan kafadarta ta hago.
   Bakin window ta tsaya dan intazo wajan tana kale kale yana dauke mata kewa.
   Garin yayi duhu,ga wata iska da take kadawa me ddi.fitilu sun haska ko ina.
  Saita tsinci kanta dasan ci gaba da kallan wajan.
 Motoci nata yawo kamar ba dare bah.
   Saida tayi kallan me isarta sannan taje tayi alwala tayi nafila tukun taji sanyi cikin ranta.nan danan bacci ya dauketa me ddi.


^~^~^~^~^~7:30am^~^~^~^~^~
  Sapna ce ta sauko cikin shirinta na tafiya makarnata,A dinning ta samu su Dad yana breakfast dan tafiya office shima zeyi.
    Bayan sun gaisa itama tayi maza tayi nata breakfast din dan ta makara.sai dariya suke mata ganin yanda take ta faman sauri.
    Tana gamawa tayi musu sallama ta fice daga gidan Dama driver na jiranta a waje suka tafi.


^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^
 Tana gama shirinta ta fito zata tafi shima lokacin zai fita.
   Ko kallan inda yake batayiba haka shima,motarta ta shige tabar gidan,shima tashi yahau ya fita yana mamakin yanda Salma ta rainasa ko kadan bata girmamashi.
Hakan yana matukar mata masa rai amma yana daf da daukar mataki koda kuwa baya so.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
  Tan tashi da sassafe ta kira Umma ta fashe da kuka.
  Hankali ummane ya tashi nan ta fara tambayar ta ko lafiya.
 "Umma ki taimakamin wallahi Kamal baya kaunata,yaci amanata,Umma dan shaye shayene ga kuma neman mata.
Kuma ko kadan baya damuwa dani wallahi jiyama ba'a gida ya kwanaba"
  "Aww! Dama haka yake,toh ki kwantar da hankalinki ennde ina raye hawaynki bazai zuba abanza bah.
  Dani yake zancan kiyi shiru yau sati kwana 10 da are afara korafi.
Zanyi maganinsa.
  Nan ta kwantar mata da hankali sukayi sallama.


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fan's club 💅🏻🌷


Written by Zeenaseer😘
[24/3 23:25] Hussaina: ©EXQUISITE ONLINE WRITERS.
🌳🌳       ⚜        🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳 
       MARAICHI❣
               NA
 Zainab Naseer Sarki
     (Zeenaseer😘)



5⃣0⃣



••••••••••••• Ran Umma ya mace sosai dan haka ta tashi ta shirya dan zuwa wajan boka.
Dan burinta shine a mallake musu Kamal sai yanda suka juya shi.
   Tana gama shirinta ta fice daga gidan.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
  Koda Fahad ya isa office abinne yaketa damunsa.
    Koda abokinsa Ahamad ya shigo ya sameshi ahaka,zama yayi tare da buga teburin gurin dan ganin abokin nasa yayi nisa cikin tunani.
   Da sauri yadan firgita tare da shafa sajansa.
   "Ya harka fito?
Ya tambayi Ahmad dake kokarin zama.
  " eh wallahi tun daxuma na tsaya signing wasu papers a kasane.
   Yana ganka cikin wani irin yanayi ko ma'am dince?
   Murmushi yadanyi tare da fadin"Ai ma'am ko matsala Malam Salma akwai rikici dan wallahi na gaji da fitinarta"
   "Uhmm! Kana bani mamaki Fahad, sai kace wanda ya rako maza.
  Tabbas anasan namiji me kula da kuma nunama iyalinsa soyayya amma bawai ka bari raini ya shiga tsakaninku.
Kai va yara ba amma mace 1jal! Tasanyaka shiga situation me mata 3 da 15 chidrns.
Gaskiya kana bani mamaki"
   Ya karashe maganar yana nunasa sannan ya koma ya jingina da kujera.
  Ajjiyar zuciya Fahad yayi tare da gyara zama "Toh kai meye shawarar kah yanzu?
  " look! Frnd,Salma tana abunda taga dama ganin ita kadaice agabanka bayan ga haka tana gani baku da kidz shiyasa.
  Ka samo yarinya budurwa wanda bata wani waye sosaiba idanta be bufe bah ka aura.
Kai sai kace"ae kafi san wayaryiya er boko"
 I see yanzu gashinan kana cin bokon"
  Shiru yayi nadan lokaci kafin yace "Nifa yanzu banga yarinyar data kwantamin bah wallahi"
  "OK! Kana nan zaune yarinyar zatazo ta kwanta maka ko!"
  Ya karashe maganar yana kallanshi.
  Dariya Fahad yayi tare da fadin "kaifa baka da mutunci"
  "Ahh! Allah kuwa kaine da wata magana,pls ka duba sosai ka samo ka kara aure malan koka samu ka huta mana"
  "Toh insha Allah zanyi kokarin yin hakan ko mum ce znsa ta dubamin yarinya"
  "Kokai fah dayama fi,dan nasan itama mum tanasan ganin en jikokin ta tunda Aisha tama wayo tana da 3kidz dinta"
 "Uhmm! Kade bari"
  Sannan suka mike suka fita danyin sallar azhr.


^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^
  Yau a gajiye ta dawo daga makaranta,dan haka tana shigowa daki ta nufa ko uniform bata cireba ta fada kan gado dan hutawa.
   Baccine ya dauketa dan tagaji sosai.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
   Lokacin da Umma ta karasa wajan bokanta,ta tanda layi dan haka saida ta kara jimawa sanan ta samu damar shiga.
   Bayan ta shiga tayimai kirarin data saba.
  Sannan ta fara gabatarme da bukatunta.
   "Boka dama na kawoma wasu kudin dan cigaba da asirin nan na wannna mahaukaciyar da kuma na yaran nan da aka rabasu da yarinyar"
   Dariya yayi tare da fadin "Angama"
   "Toh boka ina da kuma wata bukatar dan gane da mijin yata kan inasan a mallake mana shi"
   Shiru yayi nadan lokaci yana bincike kafin yace" A gaskiya yaran nan mugun hatsabibine,bazan iya tura masa aljannunaba domin nashi bakaken kafiraine,saide zan baki magani ki bata ta sakamai cikin abinci shine hanyar da za'a bi.
  Amma in aka samu matsala zaici gaba da takura mata fiye da yanda yake mata yanzu Hakan kuma na iya zama ajalinta"
   Shiru Umma tayi dan gaba daya ta rikice tasan Safiya da shiriritah karta kasa kuma Abu ya zamo matsala"
  "Shikenan abani zamuyi nasara boka"
  Wani kulli ya miko mata cikin bakar leda.
   Ansa tayi tana godiya ta biyashi kudinsa ta fice daga gurin.

    Tana fitowa kai tsaye gidan Safiya ta nufa.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
    Sai bayan la'asr Sapna ta tashi daga bccin da tayi.
   Toilet ta shiga tayi wanka Sannan tayo alwala.
   Bayan ta idar da sallah,doguwar rigarta ta dauka marar nauyi ta sanya Sannan ta Saka hula akanta ta sauko kasa dan cin abincinta.

   Kitchen ta nufa ta dauko abinci ta zauna ta faraci taji mum na saukowa itama.
   Falonta shigo ta zauna bisa kujera tana kallan Sapna da murmushi.
 "Ansha bacci  an koshi"
  Dariya Sapna tayi tare da fadin "wallahi mum na gaji yau kamar anyimin duka shiyasa ina dawowa na kwantah"
  "Ayyah dama karatu ae saidah hakuri,Allah de ya taimaka"
  "Ameen" ta fada.
Suna hira tana cin abinci Har ta gama ta maida plate din kitchen.
    Sannan ta shiga gyaggayra inda taga ya bace da wanke plates.


^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^
Salma kuwa tana tashi daga makarantar da take teaching ta shiga gari yawanta.
Dan dama shegen yawo gareta kullum bata zama agida shiya abun yafi damun Fahad.
  Da ace da antashi  2:00pm toh gida zata dawo da sauki dole sai 6pm wani tym dinma yana rigata zuwa gidan.
   Shiya sa kullum cikin rikici suke.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
     Tana isa gidan ta shiga knocking.
Safiyace ta bude mata kofar sai murnar ganin ummanta take.
   Har tsakiyar falo ta kaita ta zaunar da ita.
  Ita kuwa sai kallan er tata take batayi wani aukiba sai fari data kara.
  Ruwa da lemo ta kawo mata sai murmushi take.
  "Umma sannu da zuwa ya hanya?
 " lafiya qlau Safiya"
  "Yanaga duk kin kara ramewa ko baki lahiya Safiyyah.
 " wallahi lafiyana qlau Umma matsala daya dana gayamiki"
  "Ki kwantar da hankalinki kinji kibarsa abun cikin ranki karya zamo maki illah.
  Tunda baki rasa komaibah"

Hannu ta sanya cikin jakar ta tare da Ciro...



😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fan's club. 💅🏻 🌷



Written by Zeenaseer😘
[24/3 23:26] Hussaina: ©EXQUISITE ONLINE WRITERS
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
       MARAICHI❣
             NA
 Zainab Naseer Sarki
      (Zeenaseer😘)



5⃣1⃣


💝💝
     Life never measured by d yr u hav,but by d caring u do.
     The cheer nd Lov u shared,nd d appy pple whose hrt u hav touched.
   Tnx 4being d greatest sister ever Mumsudies.
       Nagode sosai Allah ubangiji ya barmu tare,ya kara miki lafiya,ya Kare miki yaranki ya basu ilimi me amfani.
Nagode Nagode Allah yabar zumunci.😘
                               💝💝
       Wannan shafin nakine gaba daya Maman sudies👩‍👦👄




⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
••••••••••Dakinta ta nufa dan kwanciya bacci saboda gobe ta tashi da huri.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
    Safiya daran jiya batayi bacci ba.gaba daya ta canza kama.tasha kuka harta gode Allah.
  Saida gari ya waye yayi haske sannan Kamal ya shigo dakinta.
  Yayi shirinsa tsaf da alama fita zaiyi.
  Kwance ya ganta kan gado ta kudundune jikinta.
  Karasowa cikin dakin yayi har inda take kwance.
   Kallanta yayi,fuskarta a bude duk abun hawaye ya bushe.
Idanta arufe.
  "Safiya" ya furta yana tabata.
  Tana jinsa amma tayi banza dashi saboda bakin cikin da takeji.
   Ganin hakanne yasa ya juya zai fice daga cikin dakin.
  Ahankali ta furta "dan Allah ka mikomin wayata kafin ka fita"
   Can!ya tsaya tare da yin murmushin mugunta.
Ba musu ya juyo ya dauko mata wayar ya ajje a kusa da ita sannan ya juya yayi fice warsa.
   Wayar ta dauka ta kira ummanta.
  Bayan ta daga wayarne take sanar da ita "tazo bata da lafiya"
  Hankalinta atashe ta shifa shiryawa ta nufo gidan.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
  Bayan Abba ya gama breakfast dinsa da safe.
  Dayake baifitaba ranar.
Suna zaune a falo suna hira shida mum.
 "Nikuwa ban gaya makaba"
 Kallanta yayi tare da fadin"ae yanzu saiki fada ina jinki"
   Murmushi tayi tare da fadin "Dama dankane zaiyi aure"
  Shima dan murmusawar yayi "Allah ya taimaka er gidan waye zai aura"
  "Toh! Wannan karin ba zabi,ni akace na zabo "
  "Hhhhhhh! Kefah aiki ya kamaki Allah ya bada sa'a"
  "Ameen" ta fada.
"Amma ni da ga shawarar wani Abu dana hango kamar zaiyi kyau"
  "Toh! Inajinka"
 "Me zai hana a hada su da Sapna mana"

"Sapna kuma Alhaji?"
  Ta maimaita abunda ya fada.
  "Haka fah nace miki,ina ganin zamuyi alfahari da hakan nan gaba kuma suma yaran zasuyi farin ciki da junansu"
   Shiru tayi nadan lokaci kafin tace"amma daga ganin hadari saka kama shuka sabo da Allah muyima yarinya dole, ni banasan takura mata,yanemu wata can waje gashi nan gaba yn uwanta baza suji ddi bah"
   Zama ya gyara tare da gyaran murya"kinga Halimatu,shi Aure ba'a kinsa sai innyazo da matsala,bayan haka a yanda yarinyarnan ta bamu labarinta,abun a tausaya matane.uhm!  Sabo da Allah, Nina tsaya mata tamkar mahaifinta,tayarda damu kuma muma mun yarda da ita,saboda haka kiduba kuma kiyi tunani"

Shiru rayi Bayi maganabah dan abun yasha mata kai.

"Shikenan Allah yasa hakan shine alkhari,amma abarta tukun inta gama jarabawarta sai ayi mata maganar lokacin hankalinta ya kuma kwanciya"

"Shikenan na Baku nan da wata 5lokacin ta gama jarabawar"

   Sannan suka gama yanke hukunci tare da addu'a neman sa'a.


^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^
Tana gama shirinta ba tare da wani breakfast bah,ta shirya tayi tafiyarta dan ko ajikinta.
 
   Shima daya shirya zai fita ko nemanta beyiba yayi tafiyarsa.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
   Umma tana karasowa gidan ta shiga dakin safiyar tana kiranta.

   Kwance ta tardata kan gado tana faman kukan.

"Innalillahi Safiya"
Da sauri ta karaso wajanta tare da taba jikinta.
Zafi zau! Taji.
 "Sannu kinji "

Kai kawai ta iya dagawa.
   Zaune take shirin dagata.

Wani kara ta saki tare da fadin "Umma kasana ki taimakamin"

  Sai a lokacin Umma ta gane abunda ke faruwa.
    Hijab dinta ta ajje a gefe sannan tashiga toilet ta hada mata ruwan zafi.
  Cikin dakin ta dawo tare da fadin "daure ki tashi kiyi wanka ko kyaji ddin jikin naki"

   Murya na rawa "Umma wallahi bazan taba"

Haka Umma ta sabeta har cikin Jacuzzi.
    Hani irin kara ta saki tare da dane jikin Umman tana kuka.

"Ke de Safiya anyi raguwa haihuwafa zakiyi kike wannan Abu"

"Wallahi yafi haihuwa zaf..."

"Yimin shiru sakare,zaki zauna kosaina tafi na barki ke kadai"

   "Aa wallahi zanshiga dan Allah karki tafi"

   "Toh shiga ki zauna"

"Toh zan zauna" rumtse idanunta tayi tare da rike Umman ram! Ajikinta tana ihu.

Umman ce ta rinka dannata acikin ruwan,tuntana ihu tana magiya Har ruwan yabi jikinta.

  Fitowa Umman tayi daga toilet din ta gyara dakin.
Sannan ta koma toilet din ta taimakama Safiyan ta fito.
   Kaya ta dauko mata,ta Saka sannan ta zaunar da ita gefan gado.
   Kitchen ta nufa ta hado mata tea me zafi sannan ta dauko mata paracetamol acikin jakarta.

Saida ta shanye shayin sannan tasha maganin.
   Kwantawa tayi,Umma ta rufeta da blanket.

"Sannu Safiya"

Shiru tayi mata dan gani take kamar itace sillar faruwar abun.

"Kinsande va zama zanyiba nizan tafi dan haka kina bukatar wani abun?"

"Dan Allah kafin  tafi ki soyamin ko kwaine inajin yinwa"

Tashi tayi ta nufi kitchen din ta hado mata ta zuba a flask ta kawo mata.

"Shikenan ko?

Kai ta gyada mata alamun " eh"

Hijab dinta ta sanya sannan ta rataya jikarta"nina tafi Allah sauwake sannan karki mantah da maganar kudin "

Tana kaiwanan ta fice daga dakin.

Gyara kwanciyarta tayi dan bacci take Ji.



👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
  Sapna bata dawo gida da huribah saboda lefi end class dinsu sukayi aka tsare.

Tana shigowa ta zube a falo.

"Mum sannu da gida" ta fada tana kallanta.

"Yawwa! Lafiya de ko?
Naga yau kunjima baki dawo bah.

" hmnmn! Wallahi yau fada akai cikin ajinmu,kuma frnds ne"

"Toh Allah ya kyauta ,Ade kiyaye"

"Insha Allah" ta fada sannan ta mike ta hau stairs zuwa dakin ta.



😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fan's club💅🏻🌷






Written by Zeenaseer😘
[24/3 23:27] Hussaina: ©EXQUISITE ONLINE WRITERS
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                 🌳
      MARAICHI❣
             NA
 Zainab Naseer Sarki
     (Zeenaseer😘)



5⃣2⃣
  I dedicate dis page to my lovly grp
👄AAMANEE{GOOD WISH}💅🏻🍲📚👄
   Lov u so muah....💋


⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
•••••••••Bayan Sapna tayi wanka tayi sallah,saukowa tayi taci abincinta.
Daki ta koma dan tana da Assignment.


BAYAN SATI DAYA...

Zaune Safiya take acikin falonta tana kallo.
  Dan yanzu jikinta yayi sauki sosai.
  Wayar tace tayi kara.
 Da sauri ta dauka dan tasan Umma ce ke kiranta.
  Bayan sun gaisa take tambayarta ko tasamu kudin nan.

Shiru ta danyi kafin tace.
 "Nifah Umma Kamal baya bani kudi,saide duk wani abunda zan bukata ya ajjeshi"

  "Toh Ido zaki saka masa,baya ajje kudi agaban ki"

"Wallahi ni vanta ma ganin ya fito da kudi agabana bah,dan yanzuma naji yana cewa Bauchi zamu koma"

"Bauchi kuma?

" eh haka nima naji ya fada"

"Toh shine nan Allah ya kyauta nixanyi iya kokarina innyaso na kiraki"

" toh Umma na gode sai anjima"
 Sannan ta katse wayar tana tunanin inda zata samo kudi.



Koda Umma ta shirya taje gurin boka,yanuna bacin ransa sosai kan maganar salwantar maganin nan.
  Hakade tayi bashi hakuri harya hakura.

"Toh ynzu boka nawa zamu kawa akuma taimaka mana."

  "Hanya dayace inkuma zaku iya toh"

  "Rqnka ya dade me zai hana inde ana neman bukatar hakan"

 " Wanda zaiyi muku aikin ya fada cewa saide ya sadu da ita Wanda za'a yima aikin tukun zata samu biyan bukata"

Kaban Umma ne ya fadi,da sauri ta dafe jirgi tare da zaro idanu.
Nan danan gumi ya shiga keto mata dan tashin hankali.

"Yanzu babu wata hanyar da za'a bi amagance wannan matsalar dole yanya dayace?

 " eh toh wannan itace mafi sassauci,inkuma na gaya miki sauran biyun toh"

   Jikinta har rawa yake tace "inajinka"

"Zaki kawo mana gawar yarinya er kimanin 7yrs ko kuma ki  kwana uku cikin makabarta baci ba sha kuma babu bude Ido duk abunda zakiji"

"Tashin hankali" ta fada cikin zuviyartq.

"Ranka ya dade zan iya zuwa nayi shawara?"

"An baki kwana uku karki huce hakan"

"Toh!" Ta fada sannan ta mike jiki yayi sanyi ta fita daga gurin.
Gaba daya hankalinta ya tashi dan bata tqbajin irin wannan Abu bah.
Haka tqtafi gida tana surutai kamar mahaukaciya.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
  Yau Sapna bataje makarantaba saboda kwana tayi zazzabi.
   Tana kwance a falo tana hutawa dan daga asibiti suka dawo mum na kitchen.

Fahad ne ya shigo falon da sallama,daya daga cikin kujerun ya zauna.
  Ganin Sapna a kwance kuma bata amsa mai sallamar shiba ya sashi jin haushi ya hade rai.

"Au yanzu kake tafe,Allah sa lafiya naga ba'a tafi office bah"
   Mum ta fada tare da zama a daya daga kujerun.

Zamowa yayi daga kan kujerar tare da fadin"
Mum ina yini"

"Lafiya qlau ya aiki"

"Alhmdullh" ya amsa tare da komawa ya zauna.

"Wallahi tafi yace ta tasomin gobe insha Allah"

 "Aa toh Allah ya kaimu Allah sadai lafiya"

"Wallahi lafiya qlau kawai wani saban company nine da za'a bude so ni zanjene dan ganin tsare tsaran da za'a yi can Tunisia"

"Toh Allah ya bada sa'a"

"Ameen" ya fada yana kara kallan inda Sapna ke kwance.

"Yawwa! Munyi maganar auran da Dad dinka.
Alhmdullh yaji ddi kuma ya bada goyan baya.
Yanzu yaushe zaka dawo sai ayi magana insha Allah?"

"Eh tou gaskiya in komai ya daidaita nan da 4mnth insha Allah"

"Toh shikenan Allah ya kaimu"

Kallan inda Sapna take yayi tare da fadin"wannan lafiya kuwa?"

"Harta kuma baccin kenan,wallahi fama take da zazzabi data kwanta sai bcci"

"Allah ya sauwake" mikewa yayi tare da fadin na tafi amma zan dawo da anjima dan nayima Abbah sallama maybe da asbah jirginmu zai tashi"

"Toh ka gaida Salma " Umma ta fada tare da komawa kitchen din.


^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^
    BAYAN MAGRIB..

Kayansa ya keta faman hadawa harya gama shirya trolley dinsa gaba daya.

Dakin  ta shigo tare da rungumeshi ta baya.
  Hannun ta ya zame sannan ya cigaba da abunda yake.

Tsayawa tayi tana kallanshi kafin tace "wai fahad ina zakane kaketa faman hada kaya?"
Ta fada ta kallan sa.

"Baki da tym dina shiyasa ban sanar dakeva amma tunda yanzu kin Sani zanyi tafiyane ta 4mnths"

"Watt!" Ta fada da karfi fuskarta dauke da mamaki.

"Yeah! Abunda kikaji na fada no need of repeating ma self again hope u understand"

"Look pls joke apart fahad how comes hakan zata faru I cnt believed dis"ta fada tare da juyo dashi gabanta tana huci.

Shima kallan nata yake sannan ya safa fuskarta tare da fadin " cool down bby,don't bother ur self am wid  u so pls..dnt tr.....

She shouted "enough fahad enough, wallahi babu inda zaka,inkuma zata tafin saide mu tafi tare amma kafana kafarka nd I mean it"

"Ohk! Try me nd C" key din motarsa ya dauka ya fice daga dakin.

Jagwaf! Ta fada kan gadan tare dasa hannunta ta shafe fuskarta,wata iska me zafi ta furzar tare da mikewa ta nufi dakinta.
  Katan trolley dinta ta dauko ta bude tare da dorashi saman gado, ta shiga kwaso kayan cikin wardrobe dinta tana zubawa aciki tana masifa.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
  Gaba daya jikin Umma yayi sanyi dan batasan ta yanda zata tunkari Umma da wannan maganar bah.

Gaba daya tunda ta koma gidan bata da wani sauran farin ciki.

"Yanzu meye mabita a gareni ni hauwa?
Gashi magana ta gaskiya babu abunda zai hanani mallakar Kamal ko yaki Allah"




😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
01 Amal fan's club💅🏻🌷




Written by Zeenaseer😘
[24/3 23:27] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
     *MARAICHI*❣
            *NA*
*Zainab Naseer Sarki*
    *(Zeenaseer😘)*



5⃣3⃣


*In devotion to MARAICHI fans*💋💋💋



⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
   Yana fita gidansu ya nufa.
Koda ya karasa yayi parking mktarsa awaje dan bema shiga da ita cikin gate din bah.

Da sallama ya shiga cikin falon.
  Zaune ya ga Dad shi kadai yana kallan News.

Matsowa yayi gaf da kafafunsa ya zauna.

"Barka da dare Dad"

" Barkankade Fahad ya aiki ya kokari"

"Dad Alhmdullh"

"Masha Allah Dama haka muke bukata"
Zama yayi tare da fadin"yanzu Mummynka take sanar min da maganar tafiyarka nace Allah ya taimaka"

"Ameen,Ameen"

Mum ce ta shigo falon hannunta rike da dan karamin bowl da alama fruit salad ne acikinsa sa kuma cups da spoons saman tray ta daukosu.
Saman centre table din dake tsakiyar falon ta ajje tare da zubama Dad din ta mikamai,Sannan ta zubama Fahad ta mika masa dan shima yana sansa sosai.

Guri ta nema ta zauna tare da fadin "har sallamar kenan?"

"Wallahi kuwa dan sauri take akwai abunda nakesan na karasa kafin 12am insha Allah"

"Allah ya bada sa'a"

Gaba daya suka amsa da "Ameen".

Bayan ya gama sha yayi musu sallama sannan ya fice.

Mum ce ta kalli Dad tare da fadin" kana ganin kuwa yaran nan zasu yarda da abinda muke shirin yine"

 "Kinga kawai kiyi addu'a tun yanzu kin fara karaya Haba!"

Sai lokacin Mum tayi shiru dan ita batasan takurawa Sapna dan tana kaunar yarinyar.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
Umma Safiya ta shiga kira a waya.
  Bayan ta daga,Umma ke sheda mata yanda sukayi da boka.

Itama hankalintane ya tashi dan batasan meye abinyi bah.
   "Ni yanzu tayama Kamal zai barni na fita gashi saura kwana uku mu koma bauchi"

"Kinga Safiya kawai zan koma bayan kwana uku mu sanar dashi mun janye"

"Janyewa kuma Umma?"

"Eh mana,ko ke kina da mafitane"

"Ni mafitata itace asamo yarinyar er shekara bakwai gawa inyaso basai mukai masa bah"

Shiru Umma tayi dan batasan ta inda za'a fara wannan Abu bah
"Shikenan zanyi iya bakin kokarina inga an samu nasara"

Nan sukayi sallama da juna, ko wanne da abunda yake sakawa.


GAF da sallar magariba aka aikowa Umma anyi mutuwa a makotansu kuma tasan yarinyar data mutun shekarunta baza su huce 7dinba.
   Ba karamin dadi tajiba.
  Lokacin da za'a kai yarinyar Umma tabi bayan jama'a tana ta faman tafiya kamar basu take bibah har suka isa.

Daga can nesa ta tsaya tana kallan yanda aka saka yarinyar.

Tsayawa tayi anan kofar wani gida har mutane sukabar wajan.

Bayan kamar 20mins da barin mutane daga gurun ta duba gabas da yamma,kudu da arewa amma bataga kowaba tunda babu mutane sosai a layin.

   Har wajan kabarin ta karasa tana dube dube.
   Zaman dirshan tayi ko tsoro bataji gashi gurin ya fara duhu.
   Nan fa ta shiga kwankwalar kabari,saida ta toneshi harta zo kan yarinyar.
   Likafanin ta ware ta sabata abaya ta goyata sannan ta maida gurin ta gyara tas!
   Gabanta sai faman faduwa yake dan tsoron kar wani ya ganta.

Duk abunda take me gadin makabartar na kallanta harta gama.

Da sauri tayo hanyar fita.

   "Dakata hajiya" taji an fada,wani abune ya tsarga mata tundaga kanta har tafin kafarta.

 "Kiji tsoran Allah,Dama Ashe akwai irinku da ake fada tabbas kune marassa imani,kizo har makwanta ki dauki gawa sabo da Allah ki je kiyi wani sihirin dashi,Tir! Da wannan bakin hali.
Wallahi koki maida gawar da kika dauko kokuma na tona miki asiri.

   Gaba daya kafarta tayi sanyi tama  kasa daukarta jitake kamar ta bude kasa ta shige.
  Da ker ta iya daga kafar ta juyo ta fuskanci mutumin.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
 Gaba daya Sapna bata jin ddi yanzuma jikin nata sai ahankali,duk da tasha magana.
Da ker Umma ta lallabata taci abinci kadan sannan ta bata fruit salad din tasha shinema tasha da yawa sannan tasha magani ta kwanta


^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^
  Sai kusan 12am din sannan motarshi tayi parking.

Tana zaune cikin dakinta tana jiran dawowar shi.
   Tanajin motarshi ta tsaya tayi maza ta mike ta fita falon.

  A corridor suka hadu.
Tsaki yaja " kekuma ina zaki kike faman sauri haka?"

"Kaima daga ina kake zaka wani tambayeni?"

Ratsawa yayi ta jefansa ya nufi dakinsa.
 Kayan jikinsa dan kwanciya yakesanyi ya huta.

Dakin nasa ta nufo dan yinta a kare dan ita wallahi bazai bartabah.
  Tana shigowa ya juyo ya kalleta
"If you make any step again wallahi sai ranki ya bace,batter go bck" ya fada da karfi.

Can! ta tsaya tana kallansa kamar zata fashe da kuka dan bakin ciki.

Shi kuwa cigaba da abunda yake yayi,yana gamawa ya haye gadansa ya juya mata baya dan baccin dabyakeji.

Juyawa tayi ta fice daga dakin tare da bugo kofar tana gunguni.

Juyo da Kansa yayi Kal kofar tare da fadin "Nonsense!"

Da gudu ta karasa dakinta tare da fadawa kan gado tana kuka.
   Saida tayi me isarta tana nan bacci barawo ya dauke tah.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
  Kallan me gadin take gaba daya ta shiga tashin hankali.
   "Kukan ta fara yimasa tare da fadin" dan Allah bawan Allah ka rufamin asiri zan maida yarinyar nan"

Fitilarshi ya kunna tare da fadin "muje" ya nuna hanya da fitilar......




😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*




*Written by Zeenaseer*😘
[24/3 23:27] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
     *MARAICHI*❣
              *NA*
*Zainab Naseer Sarki*
    *(Zeenaseer😘)*


5⃣4⃣


*Dedicated to UMMU HAMDAN*🍃❤🍃


*•••••••••*Gari na wayewa Umma ta saba yarinya a baya ta nufi gurin boka dabita.
 Koda ta isa,bata tarda kowa agurin bah.dan haka kai tsaye ta shige jikinta Har rawa yake ta Isar me da sakonsa.
   Yaji ddi sosai Sannan yace."Bukatarku ta mallakar Kamal zatayi ammafah bade ta juyashiba yanda takeso saide duk abunda take bukata zaiyi mata kuma bazai dinga takura mata bah"
 
   "Shikenan ranka ya dade wannan ma yayi"

Sannan ya sallameta ta tafi gida murna fal cikinta amma so tayi Kamal ya zama tamkar bawansu.

Nan da nan ta Ciro wayarta ta kira Safiya ta shaida mata duk abinda ya faru.

Ba kiramin mamaki tayi bah dan jin abinda Umman tayi bah.
    Itama tayi murna sosai kuma ta kuma yima Umman godiya kan abinda tayi mata.
  Amma bata gaya mata yanda sukayi da Bash bah.


*BAYAN WATA BIYU*

Sapna karatu ya kankama dan sun kusa fara jarabawa.
   Haka bangaran zama dasu Mum tana jin ddi sosai dan koda yaushe cikin faran tamata suke bata da wata sauran matsala.
  Kullum zataje makarantanta haka cikin gida zata huta tayi abinda taga dama.
   Har ta saba da Aisha kanwar  Fahad dayake itama a garin take aure amma ba sosai take zuwa gidaba tunda suna yawan tafiye tafiya da mijinta.
  Yaranta biyu *Walid da Walida*.
Zuwan da suka danyin Har sun shiga ran Sapna haka mamansu itama tana San Sapna tana tausaya mata.
Lokacin da Mum ta gaya mata Suna shirin hadasu Aure da Fahad taji dadi sosai dan ta tsani Salma dama.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Salma ma ba karamin dadi take jiba,kullum kaba brushin kwalta tana gantali.
Bata zaman gida sai zata kwanta dama abunda takeso kenan.
  Haka business take zubawa ba karami bama kuwa.
Bata da aiki sai kiran Fahad a waya ya turo mata kudi.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
 Shima Fahad aiki yayi nisa ya kuma fari Har yr kiba yayi kullum cikin Hutu dajin ddi.
   Suna waya dasu Mum akan lokaci harda Aisha mah kodan su Walid dan Yana dasan yara ba laifi.
  Kuma yanata faman siyayyar kayan lefe dan Mum tace yayo siyayyar sa acan ansamo mata an gama komai maybe kafinma ya dawo za'a daura auran.
Yaji ddi sosai kuma yadau alkawarin zama da wanda suka zabamai hakan shine zai zama alkhari kodan ta haifamai yara.
 Amma shi ko cikin zuciyarsa be taba kawo Sapna za'a hadashi da itaba dan iya tsana baya kaunarta.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
Umma ma anata jin dadi dan yanzu ansamu dukiya koda yaushe Safiya tana aiko mata da kudi dan an koma Bauchi kuma tana kawo mata ziyara.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Safiya an zama Business woman dan Bash ya shige mata gaba,kuma tana samu sosai.
  Haka Kamal baya hanata duk abunda taga damar yi.
  Dan asiri na aiki akansa shi kansa yana mamakin sa in yayi wani abun.
   Yaje China harsau biyu yakai enmata da yawa kuma yanzuma Yana nan yana tara wasu.
   Dukiyarshi,shaye shaye,neman mata sai abunda yayi gaba dan yayi nisa baya jin kira.
   Haka tsakaninsa da Safiya basa fada yana ansar hakkinsa duk sanda taga dama danshi baya santa kuma bazai taba santabah.
   Dama danya lalatata ya aureta kuma da lokaci yayi zai rabu da ita.

*WANNAN KENAN!*


*∞∞∞∞∞∞∞∞∞∞∞∞∞*
 Zaune take cikin falonta cike da kawayan da tayi en business sai hira ake ana dariya cikin kawayan harda Salma.

"Gaskiya Safiya kina ciniki" inji daya daga cikin matan dake zaune"

"Kuma gashi mijinki baya takura miki kiyi sana'ar ki,gashi keba kishiyaba"

Salma ce tace "ae wallahi ko ina da kishiya be isa ya hanani neman kudi nabah.

" kede Salma kiyi shiru dande baki da kishiyarne "

"Ni ai wallahi dagani ba kari duk wanda ta shigo tama fita ko wace ita" cewar Safiya,ta wani shige cikin manyan mata kodan taga tazama katuwa.


"Wallahi kin birgeni ni Fahad ko damuwa beyi da enmatabah balle ayi zancan Yana da budurwa"cewar Salma.

Daya daga cikin matan ce tace" uhm bade a shedar dan kuturu saiya shekara da yatsa"

"Habibah kenan,ai duk namijin da kikaga ya kara aure to Wallahi matarsa ce keda  aibi,ni salma namiji be isa ya hadani da wataba wallahi"

"Hmmm adaiyi mugani Allah ya kyauta"

Salma ce ta mike tare da fadin,"Nizan huce dan ina da gurin zuwa.
Kinsan ni da anyi  maganar kishiya raina ke baci"

"Toh! Ki gaida gida,sai mun hadu acan din"

Sannan suka rakota Har bakin gate ta tafi gida.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
  Sapna da Umma kusan kullum suna kasuwa siyayya.
  Itade Sapna bata taba tambayar Mum kayan waye take siyaba.

Saide in sunje guri ta tambayeta ta zabi Abu mekyau daya dace Hakan kuwa take.

Yau tunda sukaje kasuwa nasu dawo bah sai gaf da magriba.

Sun gaji likis!
Suna shigowa gida ta huce dakinta dan yin wanka da sallah ta huta.

Sai bayan ishsha sannan suka hadu a dining dan cin abinci.

Sapna ce kawai bata sauko bah.

Dad ne yace da Mum
"Ya kamata a gayama yarinyar nan abunda ake shirinyi,inta nuna bata so saimu nema masa wani koya kika gani?"

"Nima nayi tunanin hakan,saimu sanar da itan kawai"




😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷





*Written by Zeenaseer*
[24/3 23:27] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
     *MARAICHI*❣
              *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
     *(Zeenaseer😘)*


5⃣5⃣


*Dedication to HAMAGEE NOVELS GROUP. Allah ya barmu tare tnkuuuu so much fr d support*


⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
  Akwana atashi ba huya wajan Allah yau su Sapna zasu fara jarabawa.
  Ta bangaran Mum kuwa anata faman shirye shiryan biki.
Amma Har yanzu ba'a sanar da Amarya bah.
      Dan gani suke kamar zata ki yarda.


Shima Fahad yana can kullum inyace agaya masa wace Amarya ko abashi numb.sai Mum tace"kabari saika dawo"


Haka tayi ta zuwa jara bawarta hankali akwance.
Ga gyaran jiki data ke sha ,tayi kyau sosai ta kuma faske jikinta yayi sumul ga er kiba datayi danma tana zuwa makaranta.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
   Zaune suke awani baban shago da alama kaya zasu siya.

Salma ce ta kalli Safiya tare da fadin
"Keni kayan nan kamar basu da kyau ko ya kika gani"

"Gaskiya na wancan satin sunfi kyau"

"Toh gaskiya ko guri zamu canza"

"Kibari de muga sauran daze dauko" cewar Safiya.

"Gaskiya malan ka kwaso mana en Dubai su muke bukata dan Allah"

"Toh! Hajiya bari na dauko muku wani sample da akace kawowa wata Amarya inyayi muku saiku dawo gobe insha Allah za'a kawo.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
 Mum ce tace da Sapna da take kokarin parking motar tah.
   " Allah yasa mutumin nan ya kawomin kayan nan"
  "Ae tunda yace zai kawo bazai saba Alkhawari bah"

 Fitowa sukayi daga cikin motar suka nufi shagon da zasu anso kayan.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
"Kinga Safiya bara naje na dawo zan anso wannan takalman ki tsaya pls karki tafi yanzu zan dawo"

"Ohk pls karki jima kinga muna da abinyi"

"Insha Allah" ta fada tare da rataya jikarta ta fice daga shagon"


Tana shan kwana su Mum da Sapna suka nufo cikin shagon suna hira da dariya abin sha'awa.


Karaf idanun Safiya suka sauka kan Sapna, wanda ita hankalinta baya wajan.

Mamakine ya kamata,cikin zuciyar tah ta shiga sakar "Anya kuwa wannan Sapna ce,wannan daga gani en birnine,fata tafi Sapna haske da kyau kai ba ita bace amma kamar ta bace"
Sai binta take da kallo Har suka huce ta gaban tah.


Cikin shagon suka shiga da sallama,bayan sun gaisa da mutumin take tabayarshi ko "ansamo material din"

"Eh hajiya an samo amma yafi kwancan kudi danshi wannan dan 50k ne"

"Babu matsala dauko muga irinshi mum ta fada tana kallansa"

Baban shagone kowa sai harkar gabansa yake,cike yake da kayan sawa kala kala.

Tana zaune kan daya daga cikin kujerun wajan.
  Atamface ajikinta dinkin riga da skirt,sun ansheta sosai,ta sanya red din mayafi da flat din takalmi.
  Sai faman danne danne take a wayarta.


Ita kuwa Safiya tana daga can gefe axaune babu abunda take banda kallan Sapna.
   Duk wani motsinta akan idanun tah.
Sake sake kuwa kala kala cikin ranta.

Tuminne ya mikowa Mum material din.

"Yawwa" ta fada tare da ansa tana gani.

"Gsky yayi kyau Sapna ta fada tana kalan Mum din"

Murmushi kawai mum take harta hango Sapna acikinsa.

Saida suka gama siyan abunda zasu siya sannan suka mike tare da mai godiya suka fita.

Still Safiya binsu ta kumayi da kallo Har suka bace mata da gani.



Safiya! Safiya!!
Salma ke kiranta amma hankalinta baya wajan.
  "Lafiyarki kuwa,naga yanzu na varki da walwala amma na dawo na ganki da damuwa"

"Uhmm! Babu komai kawaide ina tunanin rayuwa ne"

"Toh! Tasode MU tafi karmu bata lokaci,gashican na anso takalman suna motah"

Gaba daya jikinta babu kuzari haka suka tafi,Salma nata mata bayani amma ko kadan bama ita take sauraro bah.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Tunda ta dawo gida ta kasa sukuni,dan gani take kamar Sapna ta gani.

Tana cikin dakinta gaban mudubi ta zauna tana kallan kanata tana tunani.

Tsorata ta danyi jin mutun abayanra.

Da sauri ta juyo dan  ganin ko waye.

"Aww! Ashe Kaine,wallahi nadan Ji tsoro"

Murmushi ya danyi tare da matsowa gabanta,ya dafa kafadunta tare da hada kanshi da nata suna kallan juna a mudubi.

 "Menene ke damun ki naga kamar kina cikin damuwa? Uhm! Tawan" Yana magana yana shin kissing kunnan tah.

Lumshe idanunta ta shigayi "da ker ta iya fadin ba komai"
Kawai de bana Ji.."

Hada bakinsa yayi da nata,tare da daukanta zuwa kan gado.
  Nan suka hau abunda suka saba.


*After 1hour*
Kwance suke akan gado babu kaya a jikinsu sun rufe jikinsu da blanket tana saman kirjinsa tayi shiru.

Hannu ya sanya yana shafa bayanta ahankali.
"Sweedy ki gayamin meke damun ki naga ba haka kike bah amma naga duk kin canza"

"Yaushene Kamal zeho ne?"

"Amma bance miki in muna tare ki dena ambatamin Kamal bah"

"Pls am sorry,kar muje ya kusan dawo wane kaga akwai matsala"

Peck ya manna mata a goshi tare da mikewa ya nufi toilet.

Zaune ta mike tare da shafa fuskarta da tafikan hannayanta,Ajjiyar zuciya ta sauke,tabbas zata kuma bincike akan yarinyar data gani,inkuwa Sapna ce ba makuwa itace sanadiyar rayuwarta.

Tanan zaune ya fito daga toilet din,daure da toilet a kugunta.
Itama mikewa tayi shiga toilet din itama.

Kafinta fito ya gama duk abunda zaiyi ya fice daga gidan.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
  Bayn su Sapna sun dawo daga kasuwa ta Dora musu girkin dazata yimusu sannan ta haura sama.


Sallah tayi,tana zaune saman abin sallah,wayar tace tayi kara.
  Mikewa tayi ta nufi cikin jakarta ta dauko wayar.
  Murmushi tayi dan ganin wanda ke kiranta.

"Hello zee tah ykk"

"Lafiya qlau,harkun dawo daga kasuwar?"

"Yeah mun dawo,wallahi bakiga wani material bah,Allah ki siya saiki sakashi ranar bikinki"

"Allah mutuniyar,amma ni Sappy,game da maganar dana gaya miki  na bikin ki za'ayi ba hakan bane"

"Uhm! Zee wallah kina bani mamaki,tayi zaki fadi haka,nagaya miki nifa har yanzu Mum bata yimin magana makamanciyar hakan bah"

"Wallahi Sappy baki da lafiya" ta fada tana dariya.

Itama dariyar takeyi"ke kinsan me,Wallahi ki yarda bawani aure"

"Kekoh! Inba aure za'ayi mikibah,akan me Mum zatana kaiki wajan gyaran jiki."

"Ke bazaki yarda bane,na Dora Abu a kitchen inna gama girki zankira ki take care" ta kashe tare da cillahta kan gado ta fice daga dakin dan sauko wa ta karasa girkin.




😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer*😘
[24/3 23:27] Hussaina: *©EXQUISITR ONLINE  WRITES*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
     *MARAICHI*❣
               *NA*
  *Zainab Naseer Sarki*
         *(Zeenaseer😘)*


5⃣6⃣

*Pls kuyi hakuri da mistake da nayi,na rashin fada muku ko dawa Safiya take tare,Tana tare da Bash ne abokin Kamal,sannan kuma nayi mistake da  nayi page 44 Har sau biyu,muje ahakan dan,am sorry pls.*
    *Nagode sosai da kulawarku #* *Bunch of kisses fans,lov u oll*💋




⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
     Bayan ta kammala girkin,daki ta koma dan yin sallar ishsha.
    Bayan ta idarne ta mike dan zuwa yin dinner.

Saman dining ta iske su Mum suna hira suna cin abincisu.
  Da sallama ta karasa wajansu ta nemi waje ta zauna.

"Dad sannu da zuwa" Ta fada tana murmushi

"Yawwa yr albarka,ya gidan ya exams din?"

"Alhmdullh"

"Toh masha Allah, Allah ya bada sa'a, in kin kammala cin abincin inasan ganinki a falo"

"Toh" kawai ta fada dan mugun faduwar gaban da tayi.Allah de yasa lafiya ba lefi tayi bah.
   Gaba daya jikinta yayi sanyi dan be taba kiranta hakaba kome take so saide ta gayawa Mum.
  Abincin ma kasa cinshi tayi sai cakulashi take tana jujjuya spoon din.

Mum da tun da akayi maganar hankalinta nakan Sapna ta gane hakan,itama jikinta ne yayi  sanyi dan bata kaunar abunda zai bata mata rai.

Haka tayita wasa da abincin.
  Dad ne ya fara tashi sannan Mum.
Saida ta gama jujjuyawa ko loma uku cikakkiya kasawa tayi.
  Mikawa tayi tare da kwashe kwanikan ta gyara wajan.

Jiki a San yaye ta nufi hanyar falon tare da musu sallama.
Kusa da kafafun Mum ta zauna kanta a sunkuye  tare da fadin "Gani Dad"


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Lokacin da Bash yabar gidan Kamal fitowa yayi yanata sauri dan yana da gurin zuwa.
   Wayar shice tayi kara.
Yana dagawa ya kara a kunnan sa.
"Ya mutumin yaushe zaka dawo ne"
  Kamal ne ta dayan fangaran yake magana "yh maybe gobe zan dawo dan ina da aiyikan da zanyi anan din sosai"

"Gaakiya kam ya kamata,amma nima kasan yanzu na samu kamar 6 haka da zan turo mah dawo,kuma gashi gobe zaka taho"

"Toh ai babu matsala saina bari sai nextweek na taho"

"Yawwa nace ita ta gidanka yanaji shiru ko banda itah"

"Habbbba! Rabu da ita ta tashi daga aiki,ina gajiya da ita zan turata gida namayi mamakin ganin Har yanzu muna tare"

"Gaskiyane gashi itama tana kawo mana kasuwa dan acikin yn business din da takeyi nasamu uku"

"Kaine yanzu bama wannan bane a gabana,so nake na dauko wannan yarinyar inna dawo"
Inji Kamal kenan.

"Tohni ka gayamin inda take mana,basaina dauko taba,sai na shiga amatsayin masoyi kawai tunda dama kaga ba sanina tayibah"

"Ohk kaima ka kawo shawara,tana zuwa *Excellence Model college*kuma tana daya daga cikin daliban dake rubuta exam na waec.
Zan turo maka pic dinta inyaso saika gwada.

Dariya yayi tare da fadin "gud job ma guy" saika turon bye.
Sannan ya katse wayar yana dariya tare da Jan motar da gudu.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Tsit! Falon yayi dalilin rage volume din da akayi.
  Dad ne ya cire glass din dake idansa ya ajje a gefe tare dayin gyaran murya.
   "Wato da farkode Sapna Naji dadi kware da gaske da irin yanda kike gudanar da rayuwarki,dakuma yanda kika maidamu tamkar iyayanki"

Mum de shiru tayi tana sauraran shi.

Yanda itama a bangaran Sapna hakance ta kasance.

"Kina da hankali,nutsuwa,tarbiya,ladabi da kuma biyayya,wanda dukkan wani uba na gari yake fatan danshi ya kasance hakan.
   Dalilin hakanne zamuyi miki Abu me girma da daraja wanda ya dace da rayuwar ya mace me irin shekerunki wato *AURE!*"

Dammm! Gabanta ya buga,idanunta ta rufe dan wani Abu da taji yana mata yawo gaba daya illa hirin jikinta.

"Saboda shine mutuncin ki,kuma cikar darajarki da kimarki,koda gaban yan uwanki muka maidake zasuyi alfahari da ke"

"Ji take kamar mafarki take,dawa za'a hadata auran,yaushe,kuma meyasa hakan,tambayar da takema zuciyarta kenan dake bugawa da karfi"

"Sapna baza muyi miki dolebah,wanda koda  a muslince auran dole babu kwai,ke zaki zauna dashi in kinyarda zamuyi farin cikin hakan,hakanma in baki yarda bah zamufi kowa farin ciki.
Sapna zamu hadaki aure da *Fahad*dan mu"


Gaba daya ta nemi miyan bakinta ta rasa dan ya kafe,numfashinta ne ke neman daukewa.
Da sauri takai hannunta kan kirjinta tare da dafewa idanunta arufe.
Zuciyarta sai faman bugawa take da karfi tana barazanar fitowa daga kirjinta.
Numfashinta ne ke neman daukewa.
   Cikin rantako babu abunda ke fadin banda"Allah kasa mafarki nake ba gaskiya bane"....




😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB💅🏻🌷*





*Written by Zeenaseer*😘[24/3 23:28] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
                👑👑
                   🌳
      *MARAICHI*❣
               *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
       *(Zeenaseer😘)*



5⃣7⃣



*•••••••••*Shiru falon yayi babu abunda akeji banda karan AC.
   "Sapna inkina jin nauyin fada mana toh zamu baki kwana biyu inya so saiki fada mana"

Da sauri tasa hannu ta toshe bakinta dan kukan dake kokarin kwace mata.

Nan danan ta daidaita nutsuwarta ta saita muryarta.

Gaba daya sauraran abunda zata fada suke.

Tunda tazo bata dago da kanta bah.

Ahankali ta furta"Insha Allah Zan kasance masu biyayya agareku Nagode Dad"

Gaba dayansu sunji dadin wannan furuci nata.

Dad ne ya kuma cewa"Allah ya miki albarka kije kiyi tunanin nanda jibin tashi kije"

Kasa kara furta komai tayi.
  Gaba daya ji take kamar kafarta bazata iya daukarta bah,kanta Har wani jiri yake dan ciwo.
  A daddafe ta nufi hanyar upstairs tana dafa bango Har Allah ya bata ikon kara sawa dakinta.
  Kan gadanta ta haye tare dayin rufda ciki dan hakanne kawai zai sanye ta jin sanyi aranta.
  Batasan lokacin data fashe da wani irin kuka bah.
  "Shekenan ni nashiga uku,bani da sa'a a rayuwata,me znyi da Fahad,mutumin da baya kaunata bana kaunarshi,taya zan iya rayuwar aure dashi.
Me yasa sukayi wannan tunanin,meyasa zasu yi mata wannan zabi"
  Kuka sosai takeyi marar sauti.


Har kusan *2:00am*amma bata runtsaba banda kuka da surutai babu abunda takeyi.
   Mikewa tayi ahankali ta nufi toilet.. Alwala ta dauro ta fito danyin sallah ko tasamu sauki acikin ranta.

Batan ta idar da sallar,ta jima tana addu'a hannunta ta kuma dagawa tare da fadin"Allah ni baiwar kace,Allah na kawo kukana gareka,ya Ubangiji Allah ka amshi addu'a ta.
Allah kaga xuciyata bana kaunar Fahad Allah karka sa Fahad ya amince mundin ba alkahairi bane.
"Allah kai....."
Bata karasaba wani kukan ya kuma kwace mata.
  Ni kaina ta bani tausayi saida na zubar mata da kwalla😪.


Sai bayan ta idar da sallar asbah sannan bacci ya dauketa akan sallayar.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
 Salma da huri ta tashi dan tana da zuwa makaranta.
  Bayan ta gama abinda zatayi tayi breakfast ta shirya ta fice zuwa makaranta.
 
Ita data dawo sai kuma dare dan shine ka'idar tah.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
  Shaheedah ta saki ranta Har tadanyi er kiba kuma tana jin dadin zaman katsina tunda Aunty Ummie nasanta sosai kasan cewar ita kaidaice mace agabanta kuma karama.
   Tana  zuwa makarantar ta arabi da boko,,sannan duk abunda take bukata Alhmdullh tana samu dan ba laifi suna da rufin asiri sosai.
   Saide duk lokacin da tayi sallah sai tayi addu'a wa ya Sapna Allah ya bayyanatah.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
   Yau kusan shekarar Maryam *(mommahsapna)* *8*
Agidan mahaukata cikin kulawar likitoci,kullum cikin mata magani ake.
  Saboda aciwan nata saide addu'a dan koda yaushe bata da burin da yahuce ta kashe kanta shiyasa take samun kulawa.
   Duk ta canza kama kamar ba itaba,gashi ta kara haske.
  Duk wanda ya ganta saiya xubar mata da hawayan tausayi.😪


Haka bangaran gidansu suna iya kokarinsu dan nema mata magani.
  Amma basu taba tunanin yimata maganin hausaba kamr su addu'a da sauransu dan Umma ta hanasu hakan.

Sannan sun manta shaf da wasu yaran Maryam, Har ita Aunty Najar babu kuma me taso da zancan su.

Kowa harkan gabansa kawai yake dan suma asirin na tasiri akansu.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
 *...........* *10:15am* Amma Har lokacin Sapna bata tashi daga baccin da take bah.

Ahankali Mum ta turo kofar dakin dan ganin ko lafiya Har lokacin bata fito bah,ko kunya takeji.
  Turakofar dakin tayi da sallama ta shiga,amma shiru babu amsa.
  Ga mamakinta ta duba saman gado babu Sapna,hanyar toilet ta nufo.

Can gefan gado ta hangota kwance kan abun sallah tana faman bacci.

Murmushi tayi tare da fadin "yau kuma anan ake baccin"

Karasawa tayi tare da fara tashinta ahankali.

Ahankali ta shiga bude idanunta da suka kumbura dan kuka tana saukesu kan Mum.

Da sauri ta mike zaune tare da sunkuyar da kanta.
  "Ina kwana Mum"

Murmushi tayi tare da shafa gefan fuskanta"lafiya qlau Sapna. Bacci kuma anan kodan yau baku da paper ne?"

"Uhmm! Wallahi Ina idar da sallan baccin ya daukeni anan ashe gari ya wayene haka?"

"Oya! Tashi kije kiyi wanka breakfast is ready"

Mikewa tayi ta nufi toilet dan yin wankan.

Mum kuwa bunta tayi da kallo tare da daga hannunta sama bayan Sapna ta shige toilet din.
"Allah ka tabbatar da Alkhari ta fada tana murmushi"



😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷





*Written by Zeenaseer*😘
[24/3 23:28] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜      🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
     *MARAICHI*❣
              *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
      *(Zeenaseer😘)*


5⃣8⃣

*I dedicated dis page* *U,my lovly,durlyn,Preety,adorable, talent in fact I can explain how she ix Cwt Jiddah.*
   *my best wishes to you is Miji na gari,Allah ya bar zumunci,Lov u so muah........cwthrt😘*



⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
Koda ta shiga cikin toilet din kasa wankan tayi,zama tayi jikin masan tare dayin tagumi.
   Tsawan lokaci tana nan zaune,sannan ta mike ta shiga cire kayanta,ta fara wankan.


Bata jima a wankan ba ta fito daure da towel.
Duk abunda takeyi bata da cikakken kuzari kawai tana yin shine kamar marar laka jikinta.haka take abubuwanta.

Batayi make up ba ko powder kasa shafawa tayi.
Haka ta mike ta sanya kayanta.
Sannan ta gyara gashin kanta.


Ahankali take saukowa daga kan steps din harta sauko gaba daya.
  Sannan ta nufo dining din.
Ba karamin dadi tajiba ganin babu kowa awajan.
Zama tayi kan kujerar tare dayin tagumi dan ko kadan batajin yinwa.
   Kamar karan saukowa daga stairs din take Ji.

Da sauri ta janyo flask din ta bude.
  Chips ne sai kuma farfesun naman kasu.
  Chips din tadan zuba,sai kuma tea da tadan hada.

Ahankali ta shiga ci tana shan tea din.

"Aww! Ashe harkin sauko ma kenan" Mum ta fada tana kara sowa wajan.

Murmushi tadanyi  tare da fadin "uhm na sauko,wallahi yau bacci nake jine"

"Lallai yau hutu akeji,duk baccin da akayi be isa bah,kodan kinga yau baku da papper ai gobe kyaci gidan ku"

Murmushi tayi nan danan kwallah ta taru cikin idanta.
    Dan ganin yanda Mum take kaunar ta,amma ko kadn Allah besa mata San danta bah.

"Toh ni zan fita,dan zanje anso wasu kaya.
Me gyaran jiki zata zo saita fara miki saina dawo"


Batare data dago da kanta tace "saikin dawo Allah ya kiyaye..."

Bata karasa maganar ba,kuka ya taho mata,da sauri ta sanya hannunta ta toshe bakinta dan batasan Mum Taji tah.

Nan ta dauki jakarta da key din motar tah,ta fice daga gidan.

Sakin bakin nata tayi kukan ya fito fili.
   Kuka shabe shabe danji take kamar tayi hauka.
  Tabbas dole tasan abinyi dan bata kaunar Fahad,ta tsane shi,ko muryarshi bata san ji.

Tajima akan dining din kafin ta tashi ta gyara wajan ta koma sama.

Wayarta ta dauka ta kira Zee kawarta a waya.
   Ringing daya ta daga tare da fadin "hello sappy kin tashi lafiya"

Memakon tayi magana sai kuka.

Da sauri tace "lafiya kuwa Sappy me aka yi kuma?"

Cikin rawar murya tace " Dan Allah Zee kizo pls inasan magana dake,bani da wanda zan gayawa abinda ke raina inba kebah pls ki taimaka"

"Toh insha Allah ganinan zuwa bari na karasa abinda nake,amma pls ko menene kiyi addu'a kukan bashi da amfani gani nan"

"Toh" kawai ta iya cewa sannan ta kashe wayar.

Cilla wayar tayi gefan gado,tare dayin wwanciyar reran duk kanta tana kallan ceiling dakin.
   Ita ka dai tasan yan da takeji.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
   *2:00pm* tayima Bash akofar makarantar *Excellence*dan jiran masu fitowa.

Har suka kusan karewa bega wata me kama da Sapna bah.
  Ahankali ya fito daga cikin motar tasa ya nufi wata mata dayaga ta fito daga cikin makarantar da alama malama ce.

Cikin nutsuwa yayi mata sallama.

Ahankali ta juyo da kanta tare da amsa sallamar tashi.

Bayan sun gaisane yake tambayarta "Dan Allah dama inba zaki damuba dama ina tambaya ne"

Murmushi ta danyi tare da fadin" yi tambayarka ina jinka"

"Amm dan Allah ya babu masu yin exam ne koyau babu papper?"

"Eh gaskiya ne,yau kam basu da papper sai de gobe"

"Ohk dan Allah ko karfe nawa za'a shiga kuma nawa zasu fito?"

"Zasu shiga *11:45am* sannan su gama duka *5:03pm* za'a sallame su"

"Gaskiya na gode sosai sai anjima ya fada tare da juyawa yabar wajan"

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
 A daidai kofar gidan su Sapna me Napep ya sauke Zee.
  Kudinsa ta mika masa tare da shigewa cikin gate din.
  Bayan sun gaisa da me gadin sannan ta shige cikin gidan.

Cikin falo tayi sallama tare da zama saman kujera.
Wayarta ta Ciro dan kiran Sapna ganin tayi sallama ba'a amsaba ko taji shiru.


Jin kamar anyi sallama ta Mike zaune tare da fitowa daga cikin dakin.

Ahankali ta rinka saukowa daga stairs din.

Zee ce ta dago da kanta dan ganin  me saukowar.

Murmushi tayi tare da fadin "Aww! Ashema kinji shuguwata da kiranki zanyi"

Itama Murmushin tayi mata tare da shigowa falon.

Kusa da ita ta zauna tare da fadin " sannu da zuwa"

"Ywwa!" Ta fada "wallahi duk kinbi kin dagamin hankali Allah sade ba wani abun bane ya faru?"

"Zee kitaimaka min" hawayene yafara zubowa.
"Wallahi su Mum aure zasu yi min bansan ya zanyi bah"

Murmushi tayi tare da fadin"Haba Sapna saika ce ba musulmaba,dan za'a miki aure shine duk kika bi kika daga wankalinki kamar wanda za'a kashe"

Cikin muryar kaku tace "Zee kwara a kasheni da'a auramin Fahad, Zee Fahad fah za'a dauramin"

Baki bude Zee ta tsaya tana kallan Sapna tsabar mamakinta kasa magana tayi.

"Wallahi bazan zauna ba kwara na koma gida koma mutu wa zanyi nayi"fashewa tayi da wani saban kukan.

"Amma Sapna baki da lafiya" ta fada tana nuna kanta da yatsanta.
 "Taya zaki rinka fadar irin wannan maganar,Fahad fah kikace,koba dan gidan nan bah?"

Gyada kanta tayi tana guge wayanta.

"Toh maza in bacci kike ki farka,yanzu a fadin duniyar nan akwai macan da zata ki kamar fahad amatsayin mijinta,gaskiya ki canza shawara,bama wannan bah,inde harda gaske kike taimakon da mutanan sukayi miki gaskiyane toha shine kadai abunda zakiyi musu ki Saka musu,kyautafa suka dauki dansu sabo da san da suke miki suka baki.
Haba Sappy karki  zama butulu mana ki daure kobakya sansa ki koyawa zuciyar ki"

"Amma Zee shima fah baya sona"




😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷





*Written by Zeenaseer*😘
[24/3 23:28] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳         ⚜      🌳🌳
🌳                              🌳
                👑👑
                   🌳
      *MARAICHI*❣
                  *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
      *(Zeenaseer😘)*


5⃣9⃣


*•••••••*"Baya sanki kuma shiya gaya miki haka da bakinsa?"
Zeee ta kuma tambayar Sapna.

"Aa bashi ya gaya minba amma nina fahimci hakan da..."

"Dakata" ta tsayar da itah.
"Wannan fah ba hujja bace,kuma kosu,su Mum din kika gayawa hakan ba yarda zasuyi bah,dan Allah ki kwanatar da hankalinki ki nutsu,matar mutun kabarinsa in Allah yayi ke matar sace babu fa wanda ya isa ya hana,shawarar dazan baki shine ki roki Allah ya zaba miki abunda yafi alkahairi bawai kuka bah dan Allah"

"Nagode Zee Allah kuma ya barmu tare"

"Ameen" ta fada tare da mikewa "kinga ni zan tafi dama napep na hau saboda su Mama basa nan,pls ki kara hakuri"

"Toh insha Allah,gashi kuma yanzu inzo ko ruwa baki sha ba zaki tafi"

"Babu komai kawai natafi sai gobe inmun hadu a makaranta"

Har bakin gate ta rakota tana ta faman kwantar mata da hankali sannan ta tafi.

Cikin gida ta dawo ta zauna kan kujera tare da rufe idanta.
"Allah na rukekekah ka zabamin abinda yafi alkhari"ta ke ta faman fada kenan.

Tana nan kwance akayi sallar la'asr mikewa tayi ta nufi stairs dan tayi sallah ta dora abinci.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
  Zaune take acikin gidan Safiya suna cin abinci cikin falo.

Safiya ce ta kalli Salma tare da fadin
" kinsan kuwa ranan a kasuwa wata na gani kamar kanwata data bata, gaban nin auran mu"

"Toh! Amma ke,meyasa baki mata magana bah?" Ta fada tana kallanta da mamakin tah.

"Hmmm! Ganin ta nayi da wata kamar babarta,kuma naga wannan tafi kanwata haske da wayewa sosai,shiyasa nikuma naki yimata magana dan kar na zubda mutuncina ba ita bace so rainani"

"Hakane fah amma in kina cikin garin nan itama ta nan ai zaki ganta,kuma yama za'ae mutumin daya bata a kebbi ki ganshi a Bauchi"

"Nima de haka na gani,ke meye ma na damun kaina tafi ruwa gudu"

"Hhhhhhh! Wallahi baki da mutunci"salma ta fada tana dariya.

Kofar dakin aka shiga knocking, mikewa Safiya tayi ta nufi kofar dan budewa.

Tana budewa ya rungumetah,da sauri   ta turashi baya,sannan tadan kara kofar ta juya da sauri ta kalli inda Salma take.
  Koda ta kalleta,hankalin baya wajanta tana danna wayarta.
     Ajjiyar zuciya ta ajje tare da fita ta tura kofar ta kulle.
  Yana tsaye yana faman kallanta da mamaki.
  Jan hannunshi tayi zuwa bayan gidan.

" haba Bash yanzu inda mutane acikin gidan fah,kuma ga bakuwa za zaune"ta fada ranta a bace.

"Am sorry pls" ya fada tare da hadata da bango.huyanta ya shiga shafawa yana mata magana.
 "Wallahi I can control myself Safiya kuma bansan da baki agidan bah pls kiyi hakuri"

"Matsawa tayi daga jikinsa,ohk naji ka bari anjima ka dawo amma kaga yanzu ina da bakuwa" tana kaiwa nan ta jiyu ta yi tafiyarta.

  Binta yayi da kallo harta shige cikin dakin batare data kuma jiyowaba ta kalle shi.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
  Tana kitchen tana girki taji sallamar Mum.
  Fitowa tayi tana murmushi tare da fadin "Mum sannu da zuwa" ta karasu cikin falon da Murmushin, fridge ta nufa ta dauko mata ruwa sannan ta mika mata.
   Amsa tayi tare dayimata godiya, bayan ta shane ta ajje sannan ta dubi Sapna dake gefenta,kanta a kasa tana wasa da yatsun hannuntah.

"Sapna sannu da gidan"

"Yawwa,Zainab tazo tace tana gaida keh"

"Allah sarkin ina amsawa,dama inata tunani saike kadai na bari gidan,me gyaran jikin kuwa tazo?"

"Wallahi bata zobah,har Zee ta tafi"

"Kinga irin abinda banaso kenan ko?,kazo ka bama mutun kudin aikinsa amma shi yaki bayi maka bukatunka"
Wayarta ta Ciro tare da fadin "Bara na kirata naji meya hanata zuwa.

Ringing daya biyu,ta daga,sallama tayi mata bayan sungaisa ta tambayeta abunda ya hanata zuwa.
   " wallahi hajiya banajin dadine shiyasa amma insha Allah gobe zanzo"

"Toh! Shikenan Allah ya baki lafiya,sai goban in Allah ya kaimu"

Sannan ta kashe wayar ta kalli Sapna tare da fadin "mikomin ledojin nan"

Mikewa tayi ta daukosu.

Ansa tayi tare da budewa,ta dauko wasu material masu kyau tace "kalli wannan nagani nasan zaiyi miki kyau shiyasa ba suyo miki"

"Kai Mum kayana fah sunyi yawa,gashi sai karo wasu kike"

"Hhhh! Hakane gashi Fahad ya dawo ya hada lefe bah"

Shirude tayi bata yi magana bah.

Wata sarka ta kuma fitowa da ita itama tayi kyau sosai ta kuma cewa "wannan kuma,saiki hada da wannan material din na jiya"

"Ansa itama tayi" kai gaskiya tayi kyau sosai wallahi tamafi wanda Aunty Aisha ta siyo "

"Wannan kuma itace anko din da za'a fitar"

Kallanta kawai tayi,tadanyi murmushi tare da dukar da kanta kasa.

Mikewa tsaye tayi tare da fadin"ina girki a kitchen bari na dubah"

Kitchen din ta nufa"hmmm! Sai wani shirye shirye kuke Allah yasa Fahad din karya yarda.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Washe gari da huri Sapna ta tafi makaranta dan ko breakfast din ta batayibah.
  Dan gani take kamarma tayi latti.


 👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
Yau saura 4wks Fahad ya dawo dan haka,duk yagama siyayyar kayan da zeyi,saida ya siyi 12 box na aure masu kyau.
  Sannan ya Saka kaya masu tsada dan saida yayi akwati 3 na English wear,dan yana sansu sosai.
Duk abunda ya gani saiyaga ya birgeshi,dan haka ya yanke shawarar turosu gida kafin ya karaso.

Yakuma yin kyau jikansa Har wani kalli yake saboda hutu.

Bashi da burin daya huce ya dawo yaga amaryarsa kafin biki.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
*5:00pm*tayima Kamal a kofar makarantar su Sapna yana jiran fitowar su.





😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷







*Written by Zeenaseer*😘
[24/3 23:28] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
                👑👑
                   🌳
      *MARAICHI*❣
               *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
        *(Zeenaseer😘)*




6⃣0⃣



*Pls kuyi hakuri kwana biyu banyi post bah,bani da lafiya ne amma yanzu jiki Alhmmdullh Mungode Allah ya kara Mana lafiya*💋


⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
*••••••••*Yana zaune cikin motarsa Har lokacin yana jiran fitowar Sapna.
  Wayarshi na hannunsa yana kallan pic dinta.

Dalibai nata faman fitowa amma shiru bega fitowar su bah.

Fitowa yayi daga cikin motar ya tura murfin ya rufe tare da jingina jikin motar ya harde hannayansa.

Tare suka fito ita da Zee suna murmushi da alama hira suke.
Basu tsaya a kofar makarantar bah tafiya suke da alama akwai inda zasu.

Da sauri yabi su harya cimmasu.
  Sallama yayi musu tare dashan gabansu.

Kallan juna sukayi ita da Zee kafin su maida kallansu gashi sannan suka amsa sallamar tashi.

"Dan Allah in bazaki damu bah inasan magana dake" ya karashe maganar yana mai nuna Sapna.

Da sauri ta kuma juyawa ta kalli Zee wacce itama kallan nata take.

"Malam dan Allah kayi hakuri kaga daga makrnta muke"

"Hakane na sani amma dan Allah ki saurareni wlh akwai abunda zan gaya miki pls dan Allah" ya karshe maganar yana me marairaice fuskarshi.

"Sapna ki saurareshi inyaso inkun gama saiki min magana" tana kaiwa nan ta zame hannunta daga na Sapna data riketa ta danyi gaba dasu kadan.

Kallanta ta maida gareshi tare da fadin "ina sauraranka"

Murmushi yayi tare da fadin "nagode.Amm! Sunana Bashir Abbas kumane haifaffan dan garin nan ne wato Bauchi,Wato Sapna na jima ina ganinki Allah besa na taba tunkarar ki,saida nagama bincike dangane da komai naki,a taikace de Sapna na kamu da so da kaunarki ina fatan zan samu  matsugunni cikin zuciyarki?"

Shiru ta danyi sannan tace"Am! Bashir nagode sosai da so da kaunar da kake min,amma ina me baka hakuri saboda agida anriga da anmin miji,Nagode"
Tana kaiwa nan tayi tafiyarta ta barshi a wajan tare da Jan hannun Zee sutafi.

Binta yayi da kallo yana mamakin Abinda ta gaya masa,kenan Aure zatayi.Uhmm yayi murmushi sannan ya koma ya shige motarsa.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Tana dawo wa gida sallah tayi sannan ta sauko kasa dan cin abincin tah.
   Bata tadda kowa a dining din ba da alama suna falo.
    Zama  tayi ta zuba abincin nata ta fara ci.
  Ahankali ta fara tunano magan ganun mutumin nan na dazu.
  Sai kuma taji haushin kanta,nakin amincewa da soyayyar sa,duk da bataji san nashiba cikin zuciyar,amma maybe inta gayawa su Mum tana da wanda takeso zasu iya janye maganar auranta da Fahad.

Har Mum taja kujera ta zauna,amma bata sanibah tana can tana faman tunani.

Table din tadan buga yanda zata dawo cikin haiyacinta.

Da sauri tadan zabura Har Cokalin hannunta ya fadi kasa.
 "Uhm hm Mum Sannu da gidah" ta fada duk a dan tsorace

"Inaga de da'alama papper yau akwai wahala?"

"Aiko wallahi da wahala kam shiyasa muka kai yamma bamu dawo bah"

"Toh Allah de ya kara taimakawa,inkin gama cin abincin Dad dinku na kiranki"
Dam! Gabanta ya fadi dan tasan tambayarsa zata bashi amsa.

"Toh ganinan nama gama cin abincin" mikewa tayi ta fara gyara wajan tare da maida kwanikan.

Falon ta shiga da sallama tare da zama bisa rug."Dad ina yini"

"Lafiya kalau ya exam din"

"Almdullh"

"Allah ubangiji ya bada sa'a"

"Ameen" suka amsa gaba dayansu.

"Sapna inasan Ji da bakinki karda kiji kunyata dan Allah ki fadamin gaskiya inkin amince da Auran Fahad?"

Shiru tayi ta kasa magana banda sake sake babu abunda take cikin ranta.wata zuciyar na fadin "karki cuci kanki kiyi abinda zakiyi magana zabi aka baki,kinga konan gaba yayi miki hulakanci zasu iya cewa saida suka baki zabi kikace kin amince dan haka karki yarda". Dayar kuwa cewa take " Kice kin amince,zaki kara samun gata,farin ciki,da kuma kyakkyawan gaba,ki amince Sapna"

Idanta ya cika tab da kwallah.
  Ahankali ta rumtse su kwallar ta shigo kan kumatunta "Dad Na amince" shine abunda ta furta kenan.

"Alhmdullh" duk sukayi hamdalah.

Dad ne ya kuma gyara zamansa yana me kallan Sapna da kanta yake a kasa.
"Tabbas kincika mutun Sapna kin sanyamu farin ciki kuma kin mana biyayya kamar yanda ko wani dan arziki zaiyima iyayansa,Mungode sosai Allah ya Saka da alkhari.
  Insha bazaki taba ganin ba daidaiba arayuwarki,Allah yayi miki albarka kuma ya baki yara nagari da zasu yimiki biyayya,insha zan tsaya miki aduk halinda kika shiga a duniya nan koda zan karar da dukiyata.Allah miki Albarka kuma koda kinyi aure nizan dauki nauyin karatunki ,insha Allah zaki cika dukkan burinki sannan mabanar mamakin Har gobe cikin bincike ake mungode"
Kamar yayi kwallah dan farin ciki.

Mum kuwa tama kasa magana,kamo Sapna kawai tayi tare da rungumeta.

Kamar jira itama take ta fashe da kuka.

"Kukan kuma menene Sapna?" Mum ta tambayeta.

Kara rungume Mum din tayi tare da fadin"Nima Nagode Allah ya Saka da alkhari,dan ita kanta tama rasa kukan meye takeyi na bakin cikine ko farin ciki.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*

Bayan Bash yabar wajan su Sapna gidan Kamal ya nufa kai tsaye.
  Yana cikin driving ya kirashi tare da shaida masa yanda sukayi da Sapna.
  Yayi mamaki sosai danjin anmata miji.

"Kaga Bash ka bincika da gaskene auran za'a mata anmata miji ko kawai ta fadane dan bata sanka"

"Zan bincika insha Allah dan nima nayi mamakin hakan"

"Yah ka kwantar da hankalinka, aiba aureba ko mutuwa yarinyarnan tayi saina kawo ta dan Allah ne kadai yasan irin arzikin dazan samu a kanta"

Dariya Bash ya kamayi "Gaskiya ne my Guy,nagama wata bbyn atare da Sapna Malam itama zata kawo money"

"Wannan me sauki ce munfi bukatar uwar gayyar kota wani hali aina kusa shigo".. Nan de sukayi sallama da junan shide yayi gurin Safiyar sah.





😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer*😘
[24/3 23:28] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
      *MARAICHI*❣
              *NA*
*Zainab Naseer Sarki*
     *(Zeenaseer😘)*



6⃣1⃣


*••••••••••* *K*wanci tashi ba huya wajan Allah yaune ranar da su Sapna zasu gama papers su,ya kama saura kwana uku Fahad ya dawo.

*2:00pm*🕑
  Suka fito daga cikin makarantar,kowa cikin farin ciki yake.
   Suna zaune kan wasu kujeru a wajan makarantar suna hira,me daukar Zee yazo.
  Mikewa tayi tare da fadin "ki taho mu kaiki gida tunda kinga har yanzu ba'a zo bah"

"Ke wallahi ki tafi kawai nasan yanzu zaizo"

"Toh shikenan Amarya" ta fada da zolaya.

Duka takai mata,da sauri ta shige motar tare da rufowa tana dariya.


Tana nan zaune Har Su Zee suka jima da tafiya amma shiru ba'a zo bah,tsaki tadan jah tare da kallan agogon han nunta.
Duk ta kosa ta koma gidah.

Daidai inda take zaune sukayi parking da motar.
Bash ne ya fara fitowa daga cikin motar sai Kamal ta dayan bangaran.

Kallo daya tayima motar ta kawar da kanta batare da ta kara kallan inda motar take bah.

Kamal na tsaye jikin motar sai shikuma Bash ya nufota yana murmushi.

Binta yayi da kallo ganin ta mike tayi can hanyar.
  Ahankali take tafiyar harta karasa ta bude motar da tayi parking a wajan ta shige.shima me motar janta yayi suka bar wajan.

Juyowa tayi ya kalli Kamal tare da fadin mu bisu mana.

Murmushi Kamal yayi tare da fadin "shigo mu huce kawai ni dama so nake na ganta,nasan gidan da take basaina bisu bah"

Bqdan yaso bah suka shiga suka bar wajan.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Tana isa gidan da sallama,ta ga Aunty Aisha,Mum sai kuma kawar Mum din Hajiya Bilkisu zaune a falo ga Akwatina cike anata ganin kaya.

Gaba dayansu suka amsa sallamar tare da kallan inda Sapna take.

Aisha ce ta saki buda tare da fadin"ga matar baban yaya ta iso jama'a abata guri"cike da zolaya.
  Dariya suka kama gaba dayansu.

Kamar zatayi kuka ta kalli mum tare da shagwabe fuska ta turo baki "Mum kin ganta ko"

Gaba daya suka sanya dariya "Aisha banasan shegantaka daga dawo warta harkin fara ko ki rabu da ita mana"

Juyawa tayi inda Sapna take "maza ki je kiyi wanka kici abincinki kizo kutafi salon"

Batare da tayi magana bah ta juya tayi hanyar sama tana lakwayewa kamar micijiya.

"Inyeeee aa gaskiya yaya zaisha shagwaba kaga wata salan tafiya nima ba koya in rinkawa mijina" duk suka kwashe da dariya.

Itade bata kula suba ta haye warta sama.

Hajiya Bilkisu ce dake zaune tana faman dariya tace "wallahi Aisha baki da dama,kina ganin yau ko gaidani ba'a yibah"

Mum ce tace hmmm "Sapna ko rigima"
Kallan Hajiya Bilkisu ta kuma yi tare da fadin "Hajiya Danki yayi kokari?"

"Yo acema beyiba mana wallahi Fahad yayi kokari Allah de ya sanya Alkhari ya kawo zuri'a dayyiba"

"Ameen duk suka amsa"

Kaya sunyi kyau akwatinan ma abin kallo ne sai dagawa suke suna yabawa.

Har an Buga *IV* anata faman rabawa mutane dan itama Hajiya tayi gayya ga Dad dinsa gaka zalika Fahad din.

Biki ya kama saura sati biyu.
  Anje an gyara dayan part din dake cikin gidan Fahad anyima Sapna jere nagani a fada.

Amma duk abunda ake Salma bata taba saniba,kullum da safe ta fice sai kwanyiya bacci ke maidota dan haka batasan wainar da ake tuyawa bah.

Tadesan me gidanta nakan ganya nan da kwana uku amma hakan besa ta canza zani bah.
   Babu wani gyaran gida da tayi balle gyaran dakinta haka zalika behanata fitarta bah.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Duk abunda Sapna zatayi tare da Zee sukeyi,haka duk inda zasu tare,itace abokiyarta babu wanda take gayama sirrinta sai Zee dan tana da hankali sosai.

Sai bayan magriba suka dawo daga salon din.
  Dan haka driver n hucewa yayi yakai Zee gidah.

Da sallama ta shigo falon.
  Baki ta gani gudu uku manyan mata biyu sai kuma karama mace zatayi sa'ar Sapna amma da alama matar aurece dan kamar ciki gareta.kana ganinsu kaga en uwan Mum dan suna kama sosai.

Gaba daya suka amsa mata sallamar.
  Zama tayi kan kujera tare da gaidasu.

Bayan ta gaidasu Mum tace kinga wa'en nan sune en Uwana na Katsina.
   Nuna babbar cikinsu tayi
"Wannan itace yayata Inna Abu,saikuma wannan itace babban yrta Aunty Jamila sai kuma ta nuna me cikin wannan kuma matar dantace Zuhrah.
  Dukkansu suna da fara'a sai murmushi suke.
Sunji dadi sosai ganin Sapna dan dama basu san Salma dan bata ziyar tarsu kuma ko sunje bata musu mutunci ga haushin bata haihuwa.

Aisha ce ta kalli Sapna tare da fadin "Matar yaya Anyi salon ?"

"Mummy!" Ta fada Sapna tana kallan tah.

"Aisha tunda bataso kidena fada mata mana"

"Inna Abu tace aikuwa komin kankantar ta ita matar yayance dole a kiraki da hakan"

Matsowa ta yi kusa da itan,"ya kuri muguni bazan kara fada bah"

Ahankali ta zame dankwalin.
"Wow!" Aisha ta fada ganin yanda gashin Sapna ya kara tsayi da kyau kamar ba India.

"Tabbas yaya saiya zauce anya ba kari aka miki bah?"

Mikewa tayi tare da fadin "eh naji din" ta koma kusa da Mum.

Duka sun yaba da gyaran gashin nata "masha Allah" Zuhrah ta fada dan Sapna ta kwanta mata a ranta.

Nan de akaita yaban Amarya.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Yau Fahad ze dawo gidansu ya fara cika da jama'a,daga bangaran Dad dinsa da kuma na Mum.
   Dan kowa na ta ya shi murnar kara auran da zaiyi.

Yayinda Amarya ta shiga rububi.
Ansha kunshi tayi kyau jikin nan kamar me yasha gyara yayi kyau dan gobe za'a yi kamu.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Ko kadan salma batasan Fahad na shirin kara aure bah dan haka da tasan yaune ranar dawo warsa.
  Ta zauna agida dan yimai girki.
  Tayi masa girki hadaddu masu kyau ta gyara falon da dakunan sai kamshi suke.


*6:00pm*🕕
Aka bude gate din gidansa.
   Kamar zata tashi sama dan murna.

Shima sai washe baki yake,nan aka shiga shigo da akwatina Har guda 5,gashi yakara kyau yadanyi kiba.
Sanye yake cikin English wear kamar bature ya shigo cikin gidan.

Tana fitowa daga toilet ko mai bata tsaya shafawa bah,daga ita sai towel ta fito da gudu ta nufi wajansa.
   Bayan sun gama shigo mai da kayansa yayi musu godiya ya  janyo kofar.
   Da gudu ta karaso wajan nasa tare da rungumeshi.
   Shima rungumetan yayi yana murmushi sai dariya take da murna.
  Saiyaji tausayinta ya kamashi yana tunanin yanda zatayi inya sanar mata da batun auransa.

"I miss bbyna" ta fada tana kara shigewa jikinsa,shima kara rungumetan yayi tare da fadin "miss uuu too"

"Yanzude abarni nadan watsa ruwa ko?" Ya fada yana kallan fuskanta.

Itama kallanshin take "toh muje na raka ka" tare suka shiga dakin nasa,tana makale ajikinsa.ita ta taimaka mai ya cire kayan.

Yaji dadin yanda yaga ta gyara ko ina gwanin ban sha'awa.

"Muje toh ki karasa ladanki tunda dama ba ayi kwalliya bah'ya fada yana kallanta.

Murmushi tayi masa sannan suka shiga toilet din.

Tare suka kuma yin wankan sannan suka fito.
  Ita daure da toilet dinta shikuma ya Saka bathrobe hannunsa rike da kiramin towel yana goge gashin kansa...





😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer*😘
[24/3 23:29] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
      *MARAICHI*❣
               *NA*
*Zainab Naseer Sarki*
     *(Zeenaseer😘)*


6⃣2⃣


*•••••••••* *S*ai bayan sun shirya sunyi kyau suka fito dining dan cin abinci.
    Sosai yaci abincin ya koshi dan ya yimai dadi sosai.
  Sunaci suna hira abin sha'awa.

Burinshi ya gamaci yaje gida yaga Mum dinsa,yakuma san Amaryar sa.

Bayan sun gama cin abinci,yana zaune a falo yana waya.

Ita kuma ta gyara dining din sannan ta dawo wajan sa ta zauna tare da shigewa jikinsa.

Bayan ya gama wayar ya ajjeta a gefe sannan ta kalleta "kinga yanda kikayi kyau kuwa,Ashe dama ninake takura miki ko?"

"Uhmmm! Hakade kace ni inna ganka a hanya ma bazan gane kaba dan ka koma sak bature"

Dariya yayi sosai sannan ya mike tare da fadin "bara naje naga Mum dina kinsan ina missing dinta sosai"

Ranta ta bata,ta murtuke fuska.

Murmushi yayi sannan ya koma ya zauna tare da rungumota jikinsa"haba menene kuma na bata rai,Mum dinafa nace zanje ingani ba waniba ko wata pls ki dena irin wannan in bakya nuna kulawarki agareta bazanji ddiba pls,tasoma muje tare kinji"

"Aa kawai katafi saika dawo" tana kaiwa nan ta mike tare da shigewa dakinta.

Ajjiyar zuciya ya ajje sannan ya dauki key dinsa ya fice daga gidan.

Tana shigewa dakinta gado ta fada tare da fashewa da kuka.dan gani take kamar be damu da ita bah.
   Tunawa tayi da akwatinan da taga ya shigo dasu tasan duk natane.
   Tadanji dadi,mikewa tayi ta nufi inda suke dan dubawa.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Kai tsaye gidansu ya nufa dan tsabar wani farin ciki dayake ji acikin ransa.


*Gidan Biki*
Anacan anata hira mutane cike a falan wasu na kallo wasu na hira yara kuma na wasa wasu kuma sunyi bacci.


Sapna da Zuhrah suna dakin Sapna dama can ta koma suke kwana sai Walida er gidan Aisha.

Zuhrah na zaune bakin gado.

Ita kuma tana zaune kan sallaya da alama sallah ta idar suna dan hira.



Yana karsowa aka bude mai gate ya shigo,sai gaisawa suke da sauran jama'ar kofar gidan anamai sannu da zuwa.

Mum ce ta taho hannunta rike da tray kayan abincine akai,da alama falon Dad zata kaimasa abinci.

Da sallama ya turo kofar dakin,nan mutane suka hau budah.

"Ga manmaya manya an iso manyan baki an karaso kenan barka da zuwa Ango"cewar Inna Abu dake zaune kan kujera.

Shikuwa sai faman washe baki yake yana murna.

Zama yayi tare da gaidasu,

Nan suka amsa sunata mai Allah sanya alkhairi.

Mum ma sai murnar ganin dan nata take ganin ya kara kyau kamar bashiba.

Bayan sun gama gaisawa da mutanan falon ya mike dan zuwa gaida dadin shi.

Da sallama ya shiga dakin.

Mum da Dad ne suka amsa masa,sannan ya karasa shigowa ya zauna .

Mum ce ta gyara tray din akan table din tsakiyar dakin sannan ta mike zata fita.

Dad ne ya furta " Halima dawo ki zauna mana"

Ba musu ta koma ta zauna itama.

"Dad ina yini" ya fada yana durkusar da kansa.

Cike da fara'a ya amsa "lafiya qlau ya aikin ya kuma aka baro encan"

"Wallahi Alhmdullh Dafata mun sameku lafiya"

"Lafiya kalau muke,kuma munga kayan daka turo tabbas kayi kokari Allah ya kara budi"

Dukansu suka amsa da Ameen.

"Amma Fahad kamar yanda muka sanka tun farko,munsan Har yanzu baka canzaba,saidema abunda ya kara gaba dan gane da halayanka na gari.
   Kaga yanzu dukkan wasu shirye shirye da yakamata ayishi dan gane da auran nan,Alhmdullilah yanzu anfama Babu abunda yayi saura sai sadaki da daurin aure"

Shide yayi shiru Yana sauraran Dad din nashi danshi yanzu burinsa a fada masa wace matar dazai aura.

"Alhmdullh munyima zabi nagari wanda zakayi alfahari da hakan kuma munsan zakayi mana biyayya kamar yanada ka Saba.
   Fahad" Dad ya kuma kiran sunan sa "Mun zaba maka Sapna Amatsayin matar dazaka aura"

Da sauri ya dago da fuskar sa ya kalli Mum dinsa sannan ya maida kallansa ga Dad din nasa.

"Sapna fah kace Dad"

"Kwarai kuwa da gaske haka na fada ko akwai matsala ne"

Kamar yayi kuka dan bakin ciki,Ji yayi komai ya tsaya masa cak!,
Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un yaketa mai maitawa cikin zuciyarsa.

"Dad amma ni ba'a gayamin ita zan auraba koma ni gaskiya bansan,banma kawo ita bace"

Kallan juna Dad da mum din sukayi sannan suka maida kallan su kanshi.

A fusace Mum tace "me kake nufi kenan Fahad,kagani ko Alh.abinda nake GU..."

Dakatar da ita yayi ta hanyar daga mata hannu.
  Sannan yace"koma me yake nufi be isa ya maidamu kananan yaraba,sabo da haka nayanke hukunci aure ba fashi,in an kaimasa ita ya sako mana ita tadawo gida shine zai nuna mana bamu isa bashiba"

"Wallahi Fahad kabani kunya" mum ta fada "ace yarinyar dabamu haifaba tana mace tayi mana biyayya ballan rana kai da kake namiji.

Shide shuru yayi yama rasa abinda abinda yake mai dadi kamar yai ta kwala ihu yakeji.

Shiru falon yayi na tsayin lokaci sannan yace " pls Dad ba nayi hakan bane dan na saba muku but am sorry wallahi bana santa kuma koda na aureta bazataji dadin zama da niba,gwara ku nemo wani ku hadata dashi za....."

Be gama rufe bakinsaba Mum ta mike ta kwashshi da mari ta kuma karame wani cikin zafin rai murya na rawa ta nunamai kofa tare da fadin "fita kabamu guri"

Gurin ya rike yana kallan ta sannan ya kalli Dad da idanunsa da suka rine sukayi jajir dan baccin rai.

Kamar yayi kuka yace "Mum ma...."

"Kafita nace maka tunkafin nakarama wani idiot ta fada da karfi"

Da sauri ya fice daga dakin,yana fishi ya fice daga gidan,da gudu yaja motar ya shiga horn da karfi.

A firgice me gadi ya bude masa gate din yaja motar da karfi yabar unguwar...






😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer*😘
[24/3 23:29] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
     *MARAICHI*❣
               *NA*
*Zainab Naseer Sarki*
      *( Zeenaseer😘)*




6⃣4⃣


                💞💞💞
*Dedication to Fateema Ashemi,Aunty er mitsila nd my cutee laxshmi(FIDDY G)Lov u so much.....Allah br zumunci💋*





⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
 *•••••••••* *D*a ikwan Allah Fahd ya isa gidansa dan gaba daya baya cikin haiyacinsa.yana karasowa ya danne horn.da sauri me gadi ya mike a firgice,saida ya fara dubawa dan ganin me horn dinnan.
  Ba karamin mamaki yayi bah ganin me gidan sane.
   Nan ya bude masa.
Turo hancin motar yayi ta shigo cikin gidan.
 Parking space ya karasa ya ajje motar sannan ya fito daga cikin motar.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Bayan ta karasa wajan akwatinan zama tayi,ta rinka bude su daya bayan daya tana ganin kayan ciki.
  Sai faman murna take ganin kayan da ya kwaso mata.
   Dan kanta tagaji da gani,ta rufe ta maida ta koma ta kwanta.
  Bayan ta kwanta taji karan horn,a firgice ta farka dan ganin ko lafiya.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Shigowa dakin yayi ko sallama babu ta shige dakinsa.
   Yana shiga ya bude fridge ya dauko ruwan sanyi ya kafa kansa saida ya kusan shayewa sannan ya anje sauran sai faman gumi yake,zama yayi bakin gado tare da rumtse idanunsa.
    Hannun sa ya sanya ya hargitsa gashin kansa sannan ya mike tsaye ya daki stool din dake kusa dashi yayi tsalle ya daki ango.
   Da karfi ya firta "it can be possible,why Mum why Sapna Mum"
   Ya durkusa wajan,idanunsa sunyi jajir dan bakin ciki,ziciyarshi sai faman tafasa take kamar ta fasa kirjinsa ta fito.



Gaba daya Salma ta rikice,mikewa tayi ahankali ta nufo dakinsa.
   Tura kofar dakin tayi ahankali tare da lekawa.
   Ganin Fahad durkushe ya dafe kansa ya sanyata matsowa wajansa da sauri tare da tallafo fiskarsa.
   Ga mamakinta ta saki baki  kallansa,fuskar tayi jajir hade da idan.
Harda wahaye,tunda take dashi bata taba ganin yayi kuka bah.
   Muryarta na rawa "Lafiya, menene ya faru,wani ne ya mutu"
   Banza yayi da ita dan dakinsa yayi masa nauyi.
   Ahankali ta kuma furta "Fahad ka....."
Be bari ta karasa maganar ba ya hada bakinsa da nata Har kan gado.
   Itade mamakin shi kawai take dan tasan akwai abunda ke damunsa bayasan ta sani ne kawai.
    Saida ya rabata da kayan jikin ta.
  Gaba daya ta kasa gane kansa burinta tasan meke damunsa.
   Sai de ya gama biyan bukatarsa sannan ya janyota jikinsa tare da rungumeta yana shafa mata baya.
   Nan danan bacci ya dauke tah.

Amma shi ko alamar baccin baya Ji.
  Toilet ya shiga yayi wanka yayo alwala yayi sallah sannan ya mikawa Allah kukansa.

Ya jima zaune sannan ya mike ya koma falo nan ma ya zauna dan yarasa abinda ke masa dadi.
  Tunda yake Mum dinsa bata taba marinshiba tanzu gashi ta sanadin wannan ballagazar yarinyar iyayansa  fishi da shi.

Har aka kira sallah yana nan zaune.
Mikewa yayi ya fice daga gidan.


Koda ya dawo daga masallaci be shiga dakinba  falon yayi kwanciyarsa dan baya bukatar takura.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Yaune ya kama *Alhamis* shine ranar *kamun*Sapna.

Tana kwance saman gadanta,sanye take da kayan Bacci Riga da wando kanta babu dankwali gashin kanta ya barbaje akan gadan.
Ta kamo wani silin tana wasa dashi a dan yatsanta.
   Tana kallan Ceiling dakin tana faman tunane tunane.

Da sallama Mum ta shigo dakin tare da zama bakin gadan.

Ahankali ta mike zaune tana murmushi gashin Har gadan bayanta wani sun zubo kafadunta.
"Mum ina kwana"

Itama murmushi ta maida mata tare da fadin "lafiya qlau" sai faman kallan Sapna take dan ita mugun tausayinta take.

Ahankali ta furta kamar zatayi kuka "Sapna da gaske kina san Fahad ko Dole zamu miki"

Da sauri ta dago da kanta tare da kallan fuskar Mum din,itama Mum din ta bata tausayin kanta a kasa ta girgiza kamar zatayi kukan" Aa ba dole kukamin ba,ina sansa kuma ina san na faran ta muku Har karshan nufashina"

Rungumeta Mum tayi tare da yin hawaye,hannunta ta sanya tana shafa sumar kanta.
"Allah ya miki albarka kinji ya baki yara na gari"

"Ameen" ta fa tare da kara kwantar da kanta saman kafadun Mum din tana kallan window dakin.

Tsawan lokaci tana kwance gikin Mum,
"Sapna mike kiyi wanka kiyi breakfast kinji"

"Toh" ta fada sannan ta mike ta mufi wardrobe dinta.

Mum kuwa fita tayi daga cikin dakin.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Tana tashi da safe,ta duba duba kan gadan amma batagan shiba.kuma bataji karan ruwa cikin toilet dinbah.
   Zaune ta mike,ta janyo rigarta ta sanya ta fito daga cikin dakin.
  Falo ta nufa,
Kwance kuwa ta ganshi kan kujera.
  Kallanshi ta tsaya yi,tasande tabbas akwai abunda ke damun sa dan inde ba fada sukayiba baya mata haka.

Ahankali ta karasa wajansa tare da kura masa ido tana kallan sa.
  Ahankali ya bude idansa,nan kuwa sukayi ido biyu da ita.

Murmushi ya sakar mata,itama murmushi tayi masa.

Kusa dashi ta dawo ta zauna "morng dia " yace da ita.

"Mrng" ta maida me.

"Baby"

"Naam" ya amsa mata,

Kara shigewa jikinsa tayi "pls ka gayamin abinda ke damuka,kaji"ta dago tana kallan fuskarsa.

Shiru yayi yana kallan gefe," babu komai kinji am hungry tashi muje mu hada breakfast" yana kaiwa nan ya mike tare da janyeta daga jikinsa ya nufi kitchen din itade ta kasa gane kansa.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Bayan ta fito daga toilet zama tayi ta danyi makeup sannan ta saka wata jar atamfa Riga da zani,dinki yayi mata kyau Har wata er kiba tayi kirjinta ya ciko sosai.
  Fashion dankunne ta sanya dan ita sarka bata dameta bah.
Sai bangles da tasanya red.
Tayi kyau sosai.
Jikinta ta feshe da turaruka masu kamshi.

Fitowa tayi daga cikin dakin ta saika kasa.

Nan aka fara buda sai rufe idanta da hannu take da lallan da aka mata yayi kyau.

"Masha Allah Fahad yayi sa'ar mata" wata kanwar babunsu ta fada.

Saida ta gaida kowa tukun ta zauna dan cin abinci.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Suna wasa da dariya yana dauke mata hankali dankarta damesa kan saiya sanar da ita damuwarsa.
   Har suka gama abincin.
   A cikin kitchen dina suka ka ci abinci,yana bata tana fashi.


Bayan sun gama ,ya tayata suka wanke kwanikan sannan suka gyara kitchen din.

Dama haka salma take bukata koda yaushe Fahad ya dinga nuna mata kulawa da soyayyar sa.

Tare suka gyara gidan sannan suka nufi toilet sukayi wanka..
   Bayan sun fito suna wasa da dariya suka yi shafa sannan ta zaba masa kayan dazai Saka.

Dark blue din jeans ta dauko masa da white shirt me ratsin blue.
  Yayi kyau sosai.

Ita kuma tana sanye da bathrobe ya dauke Har zuwa dakinta.
Kan gado ya ajjeta

 "Yawwa ki tsaya nima na miki kwalliya ya fada yana murmushi"

Tana kwance tana jiran irin kayan dazai zaba mata.

Wardrobe ya bude ,sannan ya dauko mata wasu English wear Riga da skirt red,dan yanasan red color.
   Sannan ya dauko mata inner wear red..








😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer*😘
[24/3 23:29] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITETS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
                👑👑
                   🌳
       *MARAICHI*❣
                *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
     *(Zeenaseer😘)*





6⃣4⃣


*Dan Allah a kara hakuri,wancanne 63 ga 64 nan.nagode💝*


*•••••••••*"Oya"ya fada tare da karasowa  wajanta.
 "Tashi mana ki Saka mo saina Saka miki"

Zaune ta mike tare da ansar pant din da bra ta saka.

Kayan ya tayata sakawa.
Sannan ya jata gaban mudubin "zauna yau zakiga kwalliyar dazan miki"

Itade dariya kawai take masa.

Nan ya dauko powder ya shafa mata,sannan ya dauko kwalli ya Saka mata.

Ya dauko lipstick ya shafa mata.

"Wow kinga yanda kikayi kyau kuwa"

Kalan kanta tayi,murmushi tadanyi ta yi kyau sosai bakamar da ba ,inta tashi kwalliya duk ta bata fuska.

Toh kin gani yanzu kinyi kyau kamar bake bah.

Wayar shi ya dauko ya shiga yi musu pic sunata dariya kala kala.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Gaba daya ranar Fahad yana tare da Salma ko gida be leka bah.
   Haka suma can basu neme shiba musamman Mum dake fishi dashi.



Bayan sallar la'asr aka hau shirin tafiya kamu.
   Duk sunyi anko sunyi kyau abin sha'awa.

Nan aka shirya Amarya tsayawa fadin kyan da tayi bata lokacine.
   Shigar Fulani akayi mata,sannan aka saka mata lifaya fara me kwalliyar Golding tayi kyau sosai.
   Nan aka nufi wajan kamu.

Ba laifi biki yayi jama'a,Amarya sai murmushi ake,duk inda tayi Zee na makale da ita.

Har kwallah tayi,dan Ji tayi dama a gida ake wannan bikin nata ga en uwanta, ga kawarta da kuma shaheedar tah.

Ansha shagali kuma komai cikin tsari suke yinsa,abunsu yayi kyau kuma ya burge kowa.

Anci an sha,ansha selfie,dan ba laifi Zee ta gayyato clssmate dinsu.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Suna zaune bayan sun gama dinner a falo.
   Wayrshi tayi ringing.
Ahankali ya dauka,duk sai jikinsa yayi sanyi dan ganin Dad dinsa ke kiransa.

Yana dagawa kafinma ya gaida shi yace "ka sameni a gida" yana kaiwa nan ya kashe wayar.

Duk sai Yaji babu DDI.
Haka nan de yatashi ya gayawa salma Dad na nemansa.

Badan taso bah,ta rakoshi Har wajan motarsa ya tafi.

Cike da mamaki take kallan dayan part din,ganin anyimai fenti an gyara shi yayi gwanin kyau.
   Ga kuma haske, gaban  tane ya fada.

Batasan lokacin da tayi hanyarba zuciyarta fal da sake sake,harta isa wajan.

Kan er barandar tahau tare da tsayawa bakin kofar,shiru tayi nadan lokaci saikuma ta koma part dinta,zuciyarta sai bugawa take.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Yau bema shiga da motar tashiba cikin gidan a kofar gida yayi parking.
   Sannan ya shigo cikin gidan.

Jin shiru falon ya sanyashi nufar falon Dad din nasa.
   Bayan ya shiga da sallama ya nemi guri ya zauna tare da gaida Dad din nasa.

Babu yabo ba fallasa ya amsa tare da fadin"Dama na kira kane ,Tunda kai baka da hankali,in sanar maka cewar gobe in Allah ya kaimu *12:00pm* in Allah ya kaimu za'a daura auranka a babban masallacin juma'a.
In kaga damar zuwa toh,sannan ranar assabar *8:00pm* za'a kawo maka matarka in kaga dama ka korota ranar da aka kaita.
Tashi ka bani waje"

Uffan be ceba ya mike yabar dakin.



Lokacin daya fito motocin mutane suka fara shigowa an dawo daga kamu.
   Haka nan badan ranshi yaso ba yake gaida mutane wasu na tsokanar sa.

Harya fito lokacin su Mum suka shigo dasu Sapna.

Ko kallan ida yake batayiba shikuma ya ganta dande be gane taba ya nufi wajan Mum.
  Kafinma ya karaso tayi tafiyarta.
Jiyayi kamar ya shake Sapna ya mutu.


Fita yayi ya shiga cikin motarsa amma ya kasa driving din.
  Zaune yayi tare da hade kansa da kujerar ya rufe idansa zuciyarsa na kuna.


Tana dawowa dakinta ta shige dan ta gaji.
   Sai Taji dama tare da Zee suka dawo dan tanasan ta zauna kusa da ita,ita kuma saitace gida zata tafi.


Kayan jikinta ta shiga ragewa.
  Duk ta cire kayan kale kalen farar rigace ajikinta me dogun hannu sai zanin filani da bata cirebah.
Kanta an mata kalba Manya wasu biyu sun zuro gefen kunnuwanta Har kasan breast dinta.
  Kaya take maidawa babu kowa cikin dakin sai ita kadai.


Fitowa yayi daga cikin motar ya nufi cikin gidan.
   Aisha ya nema tare da janta gefe yana murmushi.

"Ah yaya dama ana ganinka Ango kasha kamshi"

"Pls naji ina Sapna take ne"

"Uhmmmm! Inagani tana dakinta mana"

"Inane kuma dakinta?"

"Ahhh kaji yaya dakina mana,kai yaya jibi fah za'a kaima ita bazaka hakura bah,karsu Inna Abu suma dariya" ta karshe tana dariya.

Jiyayi kamar ya kwasheta da mari dan takaici,kota kanta bebi bah ya hucewar shi ya barta anan.

Kai tsaye dakin ya nufa.


Tana gaban mirror a tsaye ta kwance kalbar gaba guda daya tana kwance ta biyun,dukta rufe mata ido.



Ko sallama beyiba ya shigo dakin tare da Saka key.

Ta cikin mirror ta hangoshi da sauri ta juya tana kallansa gefen fuskarta daya ya rufe da gashi hannun ta rike da comb.


Yana tsaye jikin kofar ya juya baya tunda yasa key din be jiyoba dan takaicin ganin wannan er ficikar yarinyar ce matarsa abun haushi.

Nan danan yaji wata bakincikin,ya kuma shiga ransa.

Juyowa yayi tare da matsowa wajanta.

Ita kuma dukta tsorace tama rasa abinyi.






😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer😘*
[24/3 23:29] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
      *MARAICHI*❣
               *NA*
*Zainab Naseer Sarki*
    *(Zeenaseer😘)*






6⃣6⃣


*Dedication to Exquisite online writers*💋




⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
Sanye yake cikin shadda dark blue dinki yayi masa kyau sosai.
  Sai farar zanna akansa me kwalliyar blue saikuma takalmi fara da wristwatch shima silver a hannunsa.
   Yayi kyau sosai kamar bashi bah.

Ahankali yake ratsa cikin taran da Murmushi a fuskarsa.
Sai dagawa jama'a hannun yake suna gaisawa.

Har inda ya kamata ya zauna ya kara.

Ko kallan inda yake Dad beyiba,kawai abunda ke gabansa yakeyi har lokacin daurin sauran ya karasa.

Bayan an daura auranne,jama'a duk sun shaida,Dad ya sanar da walimar daya shirya wa jama'a.

Haka aka dunguma aka nufi wajan walimar.

Shikuwa Fahad babu abunda yake tunani banda Salma dan burinshi ya koma asibitin yaga halin da take ciki.

Bayan an walimar sun karaso gidan Dad ya ware da abokanan sa haka shima Fahad din.

Sai kawo kayan ciye ciye ake da shaye shaye.

Yana zaune saman kujera abokanan sa sunata zolayar sa.

Shikuwa wayarshi yaketa lallatsawa.
Cikin zuciyarshi kuma yana tuna Sapna maganar tah,tsiwarta da kuma izzarta,Murmushi ya danyi danshi mamakima take bashi er wannan abar.

Ji yayi kawai yanaso yaganta yaga wannan bakin da bashi da kunya.

Mikewa yayi tare da daukar hularsa amma ya cire Babbar rigar ya nufi cikin gidan.


Tana sama bayan sun gama cin abinci a zaune sunata hira da mutane.


Da sallama ya shigo falon.

Nan danan gurin ya rikice aka hau,buda jama'a nata yimasa Allah sanya alkhqri.

Saiya samu kansa da fara'a harda ambatan "Ameen".



Aisha ce ta leko cikin dakin da suke tare da fadin "Sapna taso Ango yazo duk kutaso za'a dauki hotona pls"

Gaba daya Sapna ta samu kanta da shiga damuwa,har Allah bata kaunar ta kuma ganinsa.

Hakan jikinta a sanyaye ta mike ta fito daga cikin dakin.

Ahankali take saukowa daga kan stairs din kanta a sunkuye.

Yana tsakiyar falon anata faman pics da jama'a bakin shi yaki rufuwa.

Har cikin falon ta karaso.

Jin kanshin turaranta yayi saboda jiya daya shiga dakinta shiyayita shaka kuma ya tabbata a jikinta kanshin yake.

Juyowa yayi itama ta daka idonta.

Karapp! Suka hada Ido dashi,da sauri ta sauke nata tare da cin magani.
Murmushi yayi dan tsiwarta na burgeshi.

"Matso mana Sappy ayi muku hoton" Zee ta fada tana dariya

Dago da kanta tayi tana kallan zee din kamar tayi kuka dan haushi.

Ahankali ta taka har wajan da yake.

Tsayawa tayi a jefansa iya kirjinsa tsayinta ya tsaya.kanta yana kallan kasa dan wata iriyar kunya takeji.

Aisha dake rike da camera tace "YAYA tadan matsa jikinka mana sai yafi kyau"

Ba tare da kalle taba ya sanya hannunsa daya ya zagaye kugunta dashi tare da matso da ita jikinsa.

Dago da kanta tayi tana kallan sa.

Ahaka Aisha taita daukarsu.

Shima juyowar yayi yana kallanta,sun jima ahaka.

Wani ihu mutanan falon sukeyi da tafi.

Da sauri suka dawo hayyacinsu.

Raba jikinta tayi da nashi tabar wajan da sauri dan kunya.

Shima Murmushi kawai yake yana gyara hular kansa.

Kowa sai cewa yake "gaskiya kun dace Allah ya bada zaman lafiya ya kawo zuri'a ta gari ameen"


Daki ta nufa tare da kullo kofar ta tsaya bakin mudubi tana kallan kanta.
Cikin ranta kuwa cewa take "gaskiya wannan bashi da kunya gaban jama'a ya kamani haka"

Kallan kugun nata tayi tare da shafa gurin daya rike.

Tsaki taja ta shige toilet danyin alwala tayi sallah.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Har kusan magriba Fahad be koma asibitin ba gashi yana cikin jama'a anata hidimar biki.

Yana cikin mutane wayarshi ta fara ringing da sauri ya dauka dan Mum din shi ke kiransa.

"Hello Mum" ya fada.

"Fahad ka turo motoci bayan issha'i akaima amaryarka kaji na gaya maka"

"Insha Allah Mum"
Katse wayar yayi ya maidata cikin aljihunsa.






Tana zaune a dakin Zuby tunda suka dawo daga asibitin takicin komai sai kuka.

Mamansuce ta shigo cikin dakin tare da fadin"Salma maza ki tashi Zuby ta kaiki gidanki dan yanzu Abbanku zai dawo kuma kinsan halinsa maza karma yazo ya fara fada"

"Kai mama wallahi ni bazan koma bah" ta fashe da wani saban kukan.

"Toh bara na kirashi na gayamasa tunda ni kin rainani"

"Aa zan tafi" ta mike tare da saka hijab dinta.

Zuby nasan yin magana amma tana tsoran mama.

Hakade mama tayi mata nasiya badan tajiba ta tafi gidan.

Suna fita suka shiga motar dan Zuby ma a kulle take.

"Wallahi YAYA karki ragamai daga shi har shegiyar matar dazai aura,kamar ki damu kanki,maybe ma kin fita kyau,gaki er birni,wqyyayiya,illimi ai kinfi karfin hulakanci"

Itade kuka kawai take.
Haka Zuby taja suka fita daga gidan.




*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Zaune take gaban Mum tana ta faman kuka Mum nata mata nasiya.
  Gaba daya an nannadeta da lifaya lemon green sai faman kamshi take.
   Bayan ta gama mata ta jata zuwa wajan Dad shima yayi mata.
   Sannan ya danka mata mukulli ahannuta tare da fadin "wannan key din motar dana siya mikine,gobe za'a kawo miki itah kinji Allah ya miki albarka,duk abunda aka miki da bakiji dadiba ki sanar mana kinji,maza Allah ya Baku zaman lafiya"

Kamar ranta zai fita dan kuka,haka ta rungume Mum tanata kuka har aka sakata a mota sannan akaja.

Itama Mum din kukan take😿







Lokacin dasu Salma suka karaso babu wajan da zasu shiga cikin gidan dan yacika da motocin kai Amarya.

Kamar Salma tayi hauka haka takeji,

Sukuwa sai faman guda suke.

Zuby ce ta fito daga cikin motar ta nufi cikin motanan wasu na shiga wasu na fitah.


Da karfi take fadin "wai wasu karnukanne suka tarema mutane hanya.

Afusace Aunty Jamila ta juyo tare da kallanta sama da kasa sannan tace " Kune karnuka,nan din gidan ubankine ke wacece mah"

Mamaki ne ya kama,Zuby ta kalli Aunty Jqmila sannan tace "hajiya gaskiya ki dena zagina,naji nan ba gidan ub.....

hannu ta daga tana mata warning," ke wallahi karkimin rashin kunya yanzu nasa amiki da iskan duka.

Nan Aisha ta taho tana fadin "lafiya Aunty Jamsy"







😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*hooo ! Anyi biki readers mu tashe*👯👯👯😂


*din din riridin Atewa*💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
*lol*😂😂😹😹😹😹😹😂😂








*Written by Zeenaseer*😘
[24/3 23:29] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳         ⚜      🌳🌳
🌳                              🌳
                👑👑
                   🌳
       *MARAICHI*❣
                 *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
     *(Zeenaseer😘)*





6⃣5⃣




*hoooooo!*  *dedication to you my MTN* *wallahi I Lov you dia Mhizdijah😂😂*
*Allah ya brmu tare musha service*💃🏻😂
*dis fr u durlyn..........muah*




⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
Tana ganin haka ta kuma takurewa waje daya.

Juyowa yayi tare da takowa wajan ta.
  Befi taku 4 xuwa 5 tsaya yayi tare da harde hannuwansa a kirjinsa yana kallanta.

Ita kuwa juyawa tayi tana kallnshi ta cikin mirror.

Tsawan lokaci babu Wanda yayima wani magana daga bisani Fahad yace "inasan ki sanar da Dad bakya san auran nan,dan hakanne kawai hanyar da zaki kubuta daga kiyayyar da nake miki"

Uhmmmm! Ta sauke ajjiyar zuciya sannan ta ci gaba da kallansa ta cikin mirror batare da jin kunya ko kuma tsoransa tace "kai meyasa bazaka sanar dasu bah,ko an gayama nima ina kaunar kane " ta fada tare da juyowa ta kalle shi cikin fada da tsiwa"

Da sauri ya dago yana kallanta dan tayi mugun bashi mamaki ganin yanda take magana.

Kara matsowa tayi har enda yake tare da fadin "Fahad nasan kai baka sona,toh nikuma kaunar Kane banayi kuma bana tunanin akwai ranar da hakan zata kasance ace ina kaunarka"

Kuka ta fashe dashi tare da fadin "ka barmin dakina ka tafi bana san ganin ka"

He ix totally speechless kallanta kawai yake dan ta mugun bashi mamaki Dama haka take.

Ba musu jikinshi a san yaye ya fita daga cikin dakin.

Daidai lokacin da yaga Mum tana tahowa da alama dakin zata shiga

Batare da ta kula saba ta huce,illa harara data watsa masa.


Sapna kuwa Fahad na fita daga dakin ta zauna bakin gado tare da fashewa da kuka.


Da sallama Mum ta tura kofar dakin,da sauri ta karasa wajan Sapna tare da fadata "lafiya meya faru,me Fahad yayi miki?" Duk ta rikice tana tambayarta.

Ahankali ta dago da jajayan idanunta ta kalli Mum din "babu abunda yayi min" ta fada tana girjiza kai "Mum kawai ina tunanin gida ne,kinga ba kowa nawa a wajan bikin nan,sai naji dama mama zataga bikina"

Sosai mum taji tausayinta,rungumeta tayi tana shafa mata kanta.

"Ki kwantar da hankalinki,insha Allah bayan auranku zamuje har gida kinji,kuma mamanki insha Allah za'a gansu ki daina kuka inde bakyaso mu bata"
Ta karasa maganar tare da dagota tana share mata hawayn da hannunta.



*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Yana fita gida ya nufa yayi parking motarsa sannan ya shiga.

Yana tura kofar falon,zaune ya ganta tana kallo,amma a zahiri ba TV take kallo bah.

Ko sallama beyiba ya nemi guri ya zauna kusa da kujerar tah.

Itama binshi tayi da kallo ganin yanda jikinsa yayi sanyi.

"Bby lafiya" ta fada tare da matsowa jikinsa.

Janyeta yayi tare da fuskantar tah "pls Salma ki bani hankalinki inasan muyi magana ta fahimta da ke pls"

Gyada masa kai tayi tare da fadin "ina jinka"

"Amma dama bayan tafiyar da nayi Su mum suka yanke shawarar zasu kara yimin aure ma'ana zasu yimin aure gobene mah daurin aur...."

Mikewa tayi tsaye tana nunashi da yatsa kafin ta yanke jiki ta fadi.

Da sauri ya mike ya nufi inda take yana fadin "Salma Salma!!"

Gaba daya hankalinsa yayi mugun tashi.

Key din motarsa ya dauka sannan ya dauketa ya fita da ita.
Cikin mota ya sakata,sannan ya shiga dama tuni me gadi ya bude masa gate nan yaja motar da gudu ya nufi asibiti da ita.



Yana isa emergency akayi da ita nan danan likitoci suka shiga bata taimakon gaggawa.

Kasa zaune yayi bare tsaye sai safa da marwa yake a corridor dakin da aka nufa da itah.

Bayan 30mins likitan ya fito tare da kiransa.

Office suka shiga suka zauna.

Sannan ya dubi fahad tare da fadin "ka kwantar da hankalinka hankalinta ne ya tashi shiya jawo mata zuciyarta ta buga da karfi hakan yasata doguwar suma amma insha Allah nan da Safiya zaku iya tafiya"

Mika masa hannun Fahd yayi sukayi masabaha"nagode Dr." Fahad yace dashi sannan ya mike ya fita ya nufi dakin da take.

Babu kowa aciki,babu abunda akeji sai karan AC ko ina shiru.

Zama yayi saman kujera tare da jinginar da kansa ,sannan yasa hannun ya dafe keyarsa gaba daya ya rasa abinda  yake mai dadi.

Tana kwance da drip a hannun ta da alama bacci take.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Washe gari bayan ya idar da sallar asbah cikin masallacin asbitin gida ya nufa dan ya kara kwanta wa dan baccin be ishe shiba.




Bashi ya farkaba sai around 10am,wanka yayi sannan ya dauki wayarsa ya kira mamansu Salma ya sanar mata suna asibiti.

Nan hankalinta ya tashi "Dan inajinde lafiya babu matsala"

"Insha Allah babu komai" yace da ita.

Ita kuma jin hakan tayi tunanin ko ciki Salma gareta cikin murna suka shiga shiri dan tafiya asibitin.

Shima asibitin ya nufa.
Koda ya je,har lokacin bata tashi ba dan haka tafiya yayi dan ya samu ko tea ne yasha.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Gidan Mum kuwa tun asbah aka tashi aka hau yin abubuwa akala kala dan bayan daurin aure Dad zaiyi walima.


Haka Sapna tunda tayi sallar asbah ta kasa komawa baccin saide kawai ta kwanta ta rufe idanunta.


Lokacin da rana ta fara fitowa,Sapna tayi wanka ta sanya atamfarta dar blue tana da zane orange tayi mata kyau dinkin yayi mata kyau kamar a jikinta akayi shi.

Nan ta fito gwanin shaawa,sai Murmushin dole take,wasu kuma sai daukarta hoto suke.



*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Lokacin da en gidansu Salma suka isa asibitin basu tanda Fahad bah.

Salma suka tanda zaune kan gado tana kuka.

Tana ganinsu ta kara fashewa da wani saban kukan dan Ji take kamar zata mutu.

Da sauri Mum din da kanwarta Zubaida(zuby) suka matso kanta.
"Lafiya ya Salma kike kuka haka" Zuby ta tambaya.

"Wayyo Allah Mamatah,Fahad ya cucene,yaci amanata wallahi bazan yafe masa bah mugu azzalumi"

"Baki da hankali Salma kike gayawa mijinki irin wannan muguyan kalamai"

"Mama kikasan abunda yayi matah" Zuby ta fada.

"Ke dallah gafaracan dake ake banasan shigar shugula" mama ta fadi tana kallan Zuby n.


"Salma me Fahad din ya miki ne ehee?"

"Mama Fahad aure ze kara,ya cuceni"

"Aure " mama ta maimaitah kalmar.

"Ai dama na fada,dama hausawa sunce rana bata karya saide uwar diya taji kunya,Salma ya gaji da halinki,gashi kinje kin cire mahaifarki maybe kumashi yara yake bukata.
Yanzu yana ina?"

Cikin kuka tace "Nima bansan inda yake bah,kuma an sallamemu"

"Toh saiki tashi mu tafi gida yazo ya daukeki,tunda shima ya tafi ya barki koya kula dake"

Haka suka mike suka tafi,ita kuwa Salma bata da aiki sai kuka.



*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Yanzu ya rage saura 10mins a daura auran Fahad da Sapna.

Kowa ya hallara Ango kawai ake jira.








😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷








*Written by Zeenaseer*😘
[24/3 23:29] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
     *MARAICHI*❣
             *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
     *(Zeenaseer😘)*






6⃣7⃣





⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
*•••••••••* "Lafiya Aunty Jamcy" Aisha ta fada tare da karasowa wajan tana kallan Zuby.

Cikin macin rai Aunty jamila tace wannan "yarinyar ke neman batamin min rai"

Tana tsaya tana wani kalle kalle tana rike da kugu.

"Rabu da ita" Aisha ta fada.
"Kanwar Salma ce muje kawai" ta fada tare da kama hannunta suka bar wajan.

Tsaki Zuby taje tare da komawa wajan motarsu.

Shiga tayi ta zauna tare da fadin "ya Salma ki sauka ki karasa gidn ki danni bazan shegiba dangin mijinki sun batan rai kar Abba ma ya dawo bana gida"

Batare data ce uffanba ta fito daga cikin motar ta nufi cikin gidan.

Ita kuma tsaki ta kuma jah sannan ta kunna motar tabar wajan.


Jama'a nata shiga suna yaba dakin Amarya dan ba karamin kyau gidan yayi bah.

Ita kuwa Sapna tana kan gado azaune fuskarta rufe har lokacin kuka take.


Tana shiga cikin gate din gidan bakin ciki ma be barta ta kalli kowa bah.
  Part dinta ta nufa tare da budewa ta shige.
Zama tayi kan kujera tare da dura hannu aka taci gaba da rusa kuka.
Kamar mahauciya haka Salma ta koma.




En kai Amarya basu jimabah,saboda Dad yace ana kaita kowa ya juyo ya dawo gida.
   Hakan kuwa manya sun Dada jah mata kunne da nasiya me shiga jiki sannan kowa ya watse.

Sapna tayi kuka kamar ranta zau fita,idanun duk sun kumbura.






Har kusan *11pm* Fahad be shigo gidanba.
   Kasan cewar ta saba bacci da huri.
  Mikewa tayi tare da sama dakin key sannan ta rage kayanta zuwa doguwa har kasa,amma hannun vest gare tah,sannan ta daure gashinta a baya.

Kashe hutar dakin tayi tayi addu'a tayi kwanciyartah.
  Dama abinka da wanda gajiya tamai yawa,tuni bacci ya dauke tah.





*11:40pm*
Lokacin Fahad yayi parking motarsa a parking space dake cikin gidan sa.
     Fitowa yayi daga cikin motar sannan ya nufi part din Salma.

Koda ya shiga babu kowa a falon,dan haka dakinta ya nufa,koda ya murda kofar sai yajishi a kulle da key.
   Ahankali ya shiga kiran sunan ta dan yasan bata bacci da huri.

Tana kwance tana faman kukan taji muryarshi.
Da hanzari ta mike zaune tana kallan kofar still ana murda tan.

Kamar taje ta bude masa,dan tana kaunar Fahad har cikin ranta.
Amma sai taji bazata iyaba dan ya yaudareta.
  Wani saban kukanne yazo mata,ta to she bakinta taci gaba da kukan tare da tura kanta cikin pillow.

Haka ya gaji da tsayuwa da kiran sunan ta ya koma dakinsa.

Dashi gaba daya yama manta da ankawo Sapna.

Wanka yayi yayi sallah tare da addu'a daya saba sannan ya hau gado.
   Shima baccinne ya dauke sa.




Yanda Salma taga rana haka taga dare,dan gaba daya ta kasa bacci ta rasa inda zata saka kanta.




*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
*7:03am*
Ahankali Sapna ta bude idanunta,juyawa tayi ta kalli agogon,da sauri ta mike dan ganin tym din gashi ko sallah bata yiba.

Toilet ta nufa tayi alwala sannan ta fito tare da saka hijab dinta ta tada sallah.






Shikuwa Fahad bayan ya dawo daga masallaci,kur'ani ya dauko dan ya karanta koya samu sanyi aransa dan damuwa tayi masa yawa.





Tana idar da sallah babu wani jira dan jitake kamar an mata duka tsiya ahankali ta sake hayewa gadanta ko hijab din ta kasa cirewa ta koma baccin ta.





Ba ita ta tashi ba sai kusan *10am* shima jin ana buga gidan ne ya sanyata tashi.

Mikewa tayi tare da gyara hijab din.
   Ahankali ta je ta bude,ganin me gadi ne ya sanyata yin Murmushi tare da gaida shi.
   Amsawa yayi sannan ya mika mata kwando tare da fadin "gashi ance akawo inji Mum"

Amsa tayi tare da fadin "Nagode" sannan ta maida kofar ta kulle ta nufi kan dinning ta anje kwandan.

Daki ta nufa tare da tube kayanta tadaura towel ta shiga wanka.

Bayan ta fito ta zauna tayi shafarta,sannan ta danyi light makeup.

Doguwar rigar material ta sanya din kin yayi mata kyau sosai gashi shape dinta ya fito,bakine da kwalliyan White nd red.ta sanya fashion earrings red.
Tayi kyau sosai sannan ta fito dan yin breakfast.






Shima Fahad din yayi wanka amma kananun kaya ya saka sunyi masa kyau sosai sai kamshi yake.


Dakin Salma ya nufa,ganin shi a bude ya sanya yayi saurin shiga amma be fantaba.
  Nan ya leka toilet still bata nan.

Kitchen ya nufa dan yasan tana can.



Ita kuwa Salma yinwa ce ta isheta,shiya sanya ta meke dan handama kanta breakfast.
   Tana tsaye cikin kitchen tana hada sandwich.

Ahankali ya shigo kitchen din tare da rungumeta ta baya.
"Bby har yanzu fishi kike dani ko"

Bazan tayi dashi taci gaba da abunda take.
   Koba komai taji dadi dan taga kamar be damu da Amarya bah.

"Pls bby talk to me pls" ya karasa maganar tare juyo da ita suna fuskantar juna.

"Baby dame zanji,inyimin auran dole gashi kema kin juyamin baya,ya kikeso nayi,nifa basan taba nake wlh am serious ina tunanin zan samu kulawa agurinki ki kwantarmin da hankali pls baby" ya karashe maganar yana marairaicewa"

Dago da kanta tayi tare da fadin "da gaske kake"

"Ohk! Baki yarda dani kenan bah"

Rungumeshi tayi tare da fadin "mun shirya amma da sharadi"

Shima matseta yayi ajikinsa "ina jinki my Majesty"

"Hahahahh" tayi dariya.
"Sharadina shine,kayimin alkawarin baza taba santaba ko kusantarta har part din tama karkaje"

Shiru yayi kafin yace "zan daukar miki sauran amma shiga part dinta ya zama dole tunda yanzu duk wani hakkinta yana kaina kuma in na saba hakan Allah zai kamani kinga ai bazaki so hakanba ko baby"

"Ohk hakane nagode ta kuma rungumeshi tana Murmushi I Lov u"

"Lov u more,yanzu ki karasa mana kinga inajin yinwa ko"

Gyada kai tayi sannan tace "kaje ka zauna ynxu znkawo maka king of hrt dina"

Peck ya manna mata a huya sannan ya fice daga kitchen din.

Kujera ya zauna tare da daukar remote ya kunna news.

Yana kalla amma cikin ranshi sai yaji yanasan zuwa yaga ya Sapna ta kwana.





Bayan ta gama yin breakfast dinta,ta mike ta gyara wajan tare dakai kwanikan kitchen.

Gidan ta shiga dubawa,ko ina ya tsaru,Murmushi tayi "Allah sarki Mamatah Allah ya baki lafiya kizo kiga gidana kiga Sapna nki tayi aure" sai hawaye ya shiga zubowa.
   Hannun tasa ta goge tana Murmushi data tuna da rayuwar su adah.





Suna gama yin breakfast din yace,baby kije kiyi wanka bara na dubo Sapna.
   Nanta hade rai.
Murmushi yayi dan yasan bataso.


Mikewa yayi ya dauki key din part din sannan ya fita.

Binshi tayi da kallo kamar ta fashe da kuka.




Dakinta ta koma ta dauki wayarta sannan ta dawo falon ta zauna.






😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷







*Written by Zeenaseer*😘
[24/3 23:30] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
     *MARAICHI*❣
             *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
     *(Zeenaseer😘)*






6⃣8⃣






*••••••••••••*Tana zaune a falo tana rike da wayar ta.
So take tayi updating din WhatsApp dinta dan batasan zaman kadaici.


Karan buga gidan ne ya sanyata mikewa tare da ajje wayar ta nufi kofar ta bude.

Yana tsaye yana kalle kalle yana jiran a bude masa kofar.

Tana budewa ta ganshi  a tsaye,
Shima kallan nata yake,matsa masa tayi sannan ya shige ya koma ya zauna kan kujera.

Kulle kofar tayi sannan ta dan jima a tsaye kafin ta koma cikin falon ta zauna.

Ahankali ta furta "Ina kwana"

"Lafiya qlau kin tashi lafiya" ya fada yana kallanta.

Kanta a sunkuye,tana kallan kasa "tace lafiya qlau" bata kara magana bah.

"Babu wata matsalar de ko,ko kina bukatar wani abunne?"yana magana tare da kura mata Ido, jikinta yayi sumul ga wani haske da tayi gashin kanta ya zubo gefe day.
   Kumawa yayi kan fuskarta,idanta a kasa eyelashes dinta Zara Zara haka dogon hancinta gwanin sha'awa sai dan karamin pink lips dinta.

Girgizamasa kai tayi alamun Aa.

Shiru nadan lokaci babu wanda ya kuma cewa Uffan sannan ya mike tare da fadin " Zan fita in kina bukatar wani abun kimin magana "

"Toh" kawai tace dashi.

Sannan ya juya ya tura kofar tare da fita ya janyo mata.

Bin shi tayi da kallo tare da tabe baki harya fita.

Wayarta ta janyo ta bude WhatsApp dinta nan messages suka fara shigo mata dayake tunda suka fara exam bata kara yiba.

Nan ta kama Murmushi dajin ddin dan Zee tace zata sanyata a grps dabyawa.

Ta jima tana cht har kusan azzahr sannan ta tashi dan yin sallah.






Bayan Fahad ya fita daga dakinsa Mita yahau ya fita dan zuwa cikin gari.
   Yana mama kin yanda yarinyar tayi kyau lokaci daya haka,danshi baya ganin ko wace mace da kyau inba Salma bah.
   Gaba daya ta fara rudashi,komai nata burgeshi yake,Murmushi yayi tare da fadin "Sapna".






Fahad na fita daga dakin tana tsaye bakin window harya fito daga part din Sapna.
   Kamar zata mutu dan kishi,lallai zata takamasa burki shine yaje yakai wannan lokacin ubanme yake zandau mataki akan sa wallahi.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Bayan sallar la'asr tana zaune a falo tana kallon wani Nigeria film.
  Taji karan tsayiwar mota,tasan ba Fahad bane shiyasa bata damu data mike bah daga inda take.


Da sallama aka turo kofar dakin nata.

Dagowa tayi tare da kallan me shigowar batare data amsa sallamar bah.

Murmushi ta fara ganin me shigowar.

Zama tayi kan kujera tare da kallan Salma" wallahi baki da mutunci daga me gida ya dawo kuma shi kenan sai a yarda mu dan rashin mutunci"

Dariya Salma tayi "wallahi Safiya bani da lafiya ne amma yanzu jiki da sauki"

Mikewa tayi tare da fadin "bara na kawo miki ruwa"

Kitchen ta nufa,Murmushi tayi "lallai inhar na sanar da su Safiya Fahd yayimin kishiya rainani zasu amma in na barsu ahaka tunda ba ganin ta zasuyi bah shikenan"
  Da wannan shawarar ta yanke hukunci bazasu Sani bah.


Nan ta hada mata en snacks da kuma  ruwa da juice ta Dora kan tray takai mata.

"Yawwa dankuwa kamar kinsan da guntun yinwana na taho"

Nan ta fara ci,suna hira suna dariya,nan take tambayarta ko zata je Dubai saro kaya ita Kamal ya barta nan da 2wks ma zata tafi.

"Uhmm! Safiya kenan ina ganin Fahad bazai bariba na gaya miki teaching din danakema kusan kullum sai mun samu matsala,business ma da kikaga inayi dande bayanan yayi tafiya amma zan gwada tabayarshi"

"Wallahi kuna bani mamaki,waiku bazaku iya juya mazajanku bah ,saide su sujuya Ku"

Itade Salma kallanta kawai take dan mamaki take bata in tafadi wani abun gashide itace karama a cikin su.
   "Toh yanzu Safiya in bai barni bah ya kikesan nayi dashi?"

"Ki dankara sunan shi gurin malami mana Haba Salma, zaki juyashi yanda ranki yake so kume kikeso shi za'a ayi agidan nan fah"

"Aeee! Salma bakisan inda gizo ke sakar bah,kwanakin baya na kusa yin hakan,Mamanmu ta gane wallahi tace na sake bata yafeba shiyasa kede kawai zan gwada inya bari sai ba miki magana"



Shiru tayi kafin tace "shikenan nizan huce Allah yasa ya barki"

"Ameen" tace, sannan ta mike "muje na rakaki"

Har wajan motarta ta rakota sannan sukayi sallama.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Bayan sallar magariba tana zaune a falo tana kallan MBC Bollywood, da alama film din da ake yayi mata kyau dan batasan abunda zai katseta.

Gidan aka fara knocking luckily kuma aka tafi tallah.

Taji dadin hakan sosai sannan ta bude kofar.

Yanzuma Fahad ne rike da Leda a hannunsa.

Shiguwa yayi saide wannan karan abakin kofa ya tsaya tare da mika mata ledar hannunsa.

Hannun ta mika ta amsa.

Hannun ya rike tare da ledar yana kallanta.
  Itama dagowa tayi tana kallansa.

"Saura kuma ki 'ki ci nida kene"

Ga mamaki ta tsaya tana kallan fuskarsa.

Janye hannun tayi daga nasa tare da sakar masa ledar,ta juya zatabar wajan.

Hannun sa ya sanya ya kamo ta gaba daya ta fada jikinsa.

A tsorace ta dago da kanta tana kallansa tana faman sauke numfashi.

Da ker ta iya furta "ni karabu dani banaci katafi da kayanka"

Kallan dan bakinta yake yanda take maganar.

"Haka kikace ko,pls kada kici kigani inna zo da safe yanda zan miki"

Yana kaiwa nan ya danka mata ledar sannan yabar dakin.

Gaba daya tama kasa tafiya tana tsaye tana kallan kofar,tana harara dan ita haushima yake bata.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Tana tsaye tana kallansa tunda yayi parking ya nufi part din Sapna.
  Gaba daya ta kumbura kamar ta bishi haka takeji harya fito.


Da sallama ya shigo tare da kulle kofar falon.

Batare daya kula taba ya ajje Leda akan dinning ya shiga dakinsa.

Wani bakin ciki taji ya tokare mata a huyanta kamar ta hadiyi zuciya ta mutu.

Shikuwa bema gantaba dan tana jikin window a tsaye.



Bayan ya jima a dakinsa sannan ya fito da alama wanka yayi danya canza kaya zuwa marrar sa nauyi.

Dakinta ya nufa amma be gantaba.

Falon ya fito.

Har lokacin tana zaune akan kujera tana faman huci kamar zakanya.


Karasowa yayi ya zauna a kusa da ita,tare da janyota jikinsa,
   Nan kuwa ta kama kuka,
"Lafiya Salma me kuma ya faru"
Tsabar kishi tama rasa abunda yasakata kukan.
   Cikin kuka tace "ya mukai dakai,amma kana dawo wa, ka wani shige part dinta bay....."

"Pls dakata mana Salma, meyasa kike nuna irin wannan kishin da yawa akan yarinyar nan kuma karama kamar Sapna, Haba wallahi saita rainaki"

"Naji ta rainani,amma ko jaririyace itah ai miji daya muke aure kaga kuwa dole nayi kishin da ita"

"Toh! Naji,amma ki rage,shifa namiji mujin mace hudu ne amma kinga abunda kike yama ketare shari'a"

Mikewa tayi tsaye tare da fadin"Fahad koma mene kace,amma bazan taba iya sharing miji da waccan yarinyar tsintacciyar mage"tana kaiwanan tabar falon.







😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer*😘
[24/3 23:30] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                 🌳
    *MARAICHI*❣
            *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
     *(Zeenaseer😘)*




6⃣9⃣


            🌷🌷🌷🌷
*Dedication to Oll my fans,tnkuuuuu so much fr ur support nd care Allah ya barmu tare*😘




⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
*•••••••••••*Binta yayi da kallo dan yaji ba dadi data kira Sapna da tsintacciyar mage.
   Mikewa yayi ya dauko ledar daya shigo da ita.
   Kazace da ice cream aciki.
  Zama yayi yaci iya cinsa ya koshi sannan ya ajje mata sauran da ice cream din danshi be dame Shiva ya dauko fresh yo dan shine abunda yafi so.

Bayan ya gama ya kashe musu hutar dakin ya nufi dakinta.
   Tana kwance akan gado da alama ba bacci take bah.
   Kusa da ita ya kwanata ya janyota amma saita mike zaune ta matsa daga kusa dashi.

"Wallahi kaide kaji kunya,dama karya kamin Wallahi kana santa,dan haka kabarmin dakina katafi wajan matarka mana" ta karashe maganar tana kuka.

"Kai kai kai kai Salma wai meyasa kike irin wannan ne eh?,kullum bakyaso azauna lafiya,ita mamatace hakkinta yana kaina in munje lahira,ni za'a tambaya bakebah,kekuma kanki kawai kika Sani bakya ta kowa,ya kikeso nayi da raina" shima ya fada cikin fishi.

"Kaikq Sani,wannan mqtsalar kace,nide na fadama Wallahi bazaka kwana a dakinan ba kaje can wajan matarka ta biya maka bukatar taka"itama ta maida mai.


Batare daya kuma kallan taba ya fito tare da shigewa dakinsa ya kullo da karfi.

Gadanshi ya fada tare da cire rigarsa ya runtse idanunsa,me zai gani inba Sapna bah tana wannan murtuke fuskar tata.
    Mikewa yayi zauna,dan yana kasa baccin" Allah sarki sai ita kaidai ko tanajin tsoro ko tayi bacci yqnxu ko taci abinci?"
   Gabadaya wannan tambayoyin yake yima nasan tabbas ba makawa san Sapna na kokarin shiga cikin zuciyarsa.
   "Ohh! Allah" ya fada  tare da kuma komawa ya kwanta,kanshin turaranta,da fuskarta kawai yake gani inya rufe idanunsa.
   "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" yaketa faman fada "taya hakan zata faru dani,taya san yarinya far daya haka taya taya hakan ma zata yiyu?
Tabbas xuciyarshi batamai adalciba inhar ta kamu dasan Sapna"

Toilet ya nufa yayo alwala dan yin nafila dan ko kadan baya jin baccin mah.






Bayan ta kullo kofar kan dining ta ajje kayan dan basa gabanta.
   Zama tayi dan karasa kallan film din amma ta kasa dan duk ya bata haushima.
   Kashe kayan kallan tayi sannan ta dauki wayarta ta koma dakinta.
   Wanka tayi dan ta saba mundun zata kwanta sai tayi wanka.
   Bayan ta fito daga wankanne ta sanya wando mai laushi na bacci iya gwiwa da riga me hannun shimi sannan ta saka hula akanta ta kwanta tare da dauko wayar ta dan ta yi cht.

  Tana bude data sakonni suka fara shigowa.
  Nan ta shiga gro din en makarantar su dan ganin anata faman hira.
  Cikin sa'a kuwa taga zee online.

Da sauri ta nufi PC ta mata magana.
   
           *°°°°°°°°°°°°°*
Slm

*Zee:*😳me Amarya take yanzu a online.

*Sapna:*☺Abunda kikeyi.

*Zee:*Tafdi jan ,toh ya kk

*Sapna:*qlau Wallahi, shine kika ki zuwa koh.

*Zee:*😂Nazo namiki me kuma bamaki da lfy.

*Sapna:*🙄Uban bani da lafiya,ke wlh yau ni kadai na yini wlh

*Zee:*hmm nikam na kasa gane wannan Lov naku keda Angon naki

*Sapna:*kede kika Sani me ruwana dashi yana can ina nan.

*Zee:*Sappy

*Sapna*Naam

*Zee:*Wallahi Wallahi zan baki shawara amma inkin yarda.
   Yanzu an rigada an aura miki Fahad.
 Koda ace shi baya sanki ke zaki iya janyo soyayyar zuwa gareki Haba dan Allah saikace ba mace bah kamar baki da ilimi,kinafa da kishiya dadi zata rinkaji in taga be damu dakeba.
Ko wa da kika gani da kaddarar sa,Allah yayi Fahad shine abokin rayuwarki,me yasa baza ki rungumeshi amatsayin mijin kibah,kiyima kanki fada mana kinji kawata😘.

*Sapna:*Hmmm toh yanzu ya kikesan nayi.

*Zee:*ywwa shiyasa nake kaunarki,ki daukeshi matsayin mijinki kar kiji kunya dan girman Allah, nasan maybe tunda aka kawo ki be kwana a dakin bah ko?

*Sapna:*Eh

*Zee:*kar kiji kunya gobe in yazo dakinki ki sanar dashi araba girki dan manzan Allah karkiji kunya pls kawata.

*Sapna:*Toh

*Zee:*Wallahi zakisha mamaki,shima zaiji dadin hakan saboda kin nunamai gaskiya kuma karkinajin kunyarnan taki da yawa pls,ki zauna kima mijin ki biyayya insha Allah zaki zamo star 🌟 din Fahad😹😹

*Sapna:*Hegiya zee wai aina kikasan abubuwan nan ne 😂😂

*Zee:*🙈Zauna nan Wallahi garin kallan ruwa kwado ya miki Ido,pls kawata a dage,kuma zan dinga turo miki abubuwan da dama da girke girke insha Allah.

*Sapna:*wow gaskiya Nagode sosai Allah ya barmu tare.kuma ke ma Allah baki miji na gari.

*Zee:*ywwa Ameen nima Nagode saida safe.
             *°°°°°°°°°°°*

Sannan sukayi sallama dan Sapna taji ddi kuma tana alfarahi da Zeeee☺


😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer😘*
[24/3 23:30] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
                👑👑
                  🌳
      *MARAICHI*
              *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
     *(Zeenaseer😘)*





 7⃣0⃣





*Dedication to UMMIE JAFAAR*🤕




*••••••••••*Washe gari bayan ta idar da sallah komawa tayi ta kwanta dan bata kwanta da huri bah kasan cewar tadanyi cht.


*★★*

Bayan Fahad ya dawo gada masallaci,tsayawa yayi yana kallan part din Sapna dan Ji yake kamar ya je amma kuma saiya fasah.
  Haka ya nufi part dinsu cike da zumudin gari ya waye ya je ya ganta.


*★★*
Salma Tana tashi ta nufi kitchen dan hada breakfast dan bata san fahad ya fito ya sameta a nan.
   Tea kawai ta hada sannan ta dafa indomie.
  Tana gamawa ta nufi dakinta dan karyawa.


*★★*
*9:56am* ya fito daga toilet din,dama yanzu hutu yake na 1mnth agida.
   Dan haka cikin shadda fara tas yayi shigar,din kin boda yayi masa kyau sosai, wristwatch kawai ya saka sannan ya feshe jikinsa da turare dan yanasan ya je ya gaida su Mum.
   Bayan ya fito falon bega kowa bah.
   Da har zai fita sai kuma ya fasa ya nufi dakin Salma.

Tana zaune tana cin indomie dinta akan gado.
  Da sallama ya shiga tare da zama gefan gadan yana kallanta.

Murmushi ya danyi tare da furta "ina kwana bby"

Bazan tayi dashi taci gaba da cin abin cin tah batare data ko kalli inda yake zaune fah.

"Good" ya fada tare da dage kafadunsa alamun be damu bah.

"Nizan je gida in kina da bukatar wani abun ki sanar dani dan maybe sai yamma zan dawo"

Shiru tayi kafin tace ba tare data kalleshin bah "inasan magana da kai amma saika dawo din"

Mikewa yayi tare da manna mata Peck a kumato "bye Lov"

Sannan ya fice daga cikin dakin nata.


*★★*
Yauma Mum ta aiko mata da Breakfast dama kuma yinwa ta ki Ji dan jiya bataci komai bah ta kwanta.
   Koda taxo ta amshe abinci dame gadi ya kawo bata kulle kofar bah saboda kiran da ake mata a waya.

Bayan ta ajje kwandan saman dining ta shiga daki tare da rire hijab dinta da hular.
   Gashinta ya zubo gadan baynta.
  Toilet ta shiga danyin brush.


*★★*
Yana fitowa daga part din Salma wajan Sapna ya nufa.
   Yana tura kofar ga mamakinsa ya jita a bude shiga cikin falon yayi babu kowa sai kwando kan dining da kuma ledar jiya daya kawo matah.

Murmushi yayi "lallai ma yarinyar nan kenan bata ci abinda na kawo matan bah.

Dakinta ya nufa dan yasan tana ciki.



Tana gama brush din ta fito daga toilet din ta nufo kofa zata fita dan yinwa take Ji.


Gaba daya ta jita kan kirjin mutun.

A tsorace ta furta " Innalillahi "

Shikuwa rukota yayi tare da matse tah a jikinsa.

Gaba daya ta tsorata dan haushi kamar ta fashe da kuka.

Zuciyarta sai bugawa take da karfi.

Jikinta ta kwace taja baya tare da fadin "ina kwana"

Be amsa mata ba yaci gaba da shigowa dakin yana kallan ta.

Kanta na gasa yana step forward ita na backward har ya kai karshan gadansu ta fada kan gadan ta zauna tana kallansa.

Biyota yayi harya kan gadan ta kwanta shima ya mata rumfa da hannayansa.

Da sauri ta rumtse idanun tah tare da kautar da kanta dan atunaninta kiss zai matah.

Ahikuma sai kallan fuskarta yake,

Tsawan lokaci suna kwance ahaka.

Da ker ta iya bude baki idanta a rufe tare da fadin "dan Allah ka barni na tafi inajin yinwa"

Shiru yayi yana kallanta still "baki da kunya ko,meyasa bakici abinda na kawo miki jiya bah"

"Shiru tayi bata bashi amsa bah"

Shinshina mata huya ya shiga yi yana shafa fuskarta.

Cikin rawar murya "dann Allah kayi hakuri wlh zanci pls "

Dagata yayi batare daya kalleta bah ya fitace daga dakin ya koma falo ya zauna kan kujera.


Yana fita ta fashe da kuka,tare da to she bakinta,hawayene ya shiga bin kumatuntah.
   Wannan wani irin abune Allah kabani ikon yin biyayya fa mijina amma narsa meyasa bana san Fahad.

Toilet din ta koma ta cigaba da kukan sannan ta wanke fuskarta ta fito.


*★★*
Tunda ya zauna a falon ya dora hannayansa akansa tare da hargitsa gashin kansa.
   Tabbas yana gaf da haukace,shine ya yakejin wani Abu akan Wata ba Salma bah,
  Yanzu ya tabbata san Sapna ya gama shigarshi abinda ya rage masa ya samo tatah dan yaga kamar da gaske bata kaunarsa.

Yana cikin wannan tunanin ya Ji karan plate.


Sanye take da hijab tana gaban dining tana zuba abinci.

Taso wa yayi tare da Jan daya daga cikin kujerun ya zauna"Nima asammin abincin pls"
Ya fada yana kallan fuskarta data daure babu alamun dariya.taso ta sashi dariyar amma ya maze.

Batace dashi uffan ba ta zuba masa a abinci chips ne da egg sai farfesun kifi,sannan ta hada mai tea.

Sannan ta dauki nata zata tafi daki.

"Sapna!" Ya fada sunan tah,
cak! ta tsaya tana jiran abunda zai fada,

"Ko ki dawo ki zauna kici agabana ko kuma ki zo ki bani abaki inyaso saiki tafi dakin"

Kamar zatayi kuka ta dawo ta zauna sannan ta saka cokalin amma taki cin abincin tea din kawai take sha.

Kallanta yayi batare daya mata magana bah yaci gaba dakin abincinsa.
Yanayi yana kallanta.


Har ya kusan cinyewa amma bata koyi cokali daya bah.

"Naga da alama yau ni akesan na bada abincin nan abaki da kaina"

Tasan zai iya dan bashi da kunya kam,da sauribta dauki lokacin ta fara ci tana hawaye dan ita ya takura ta.

Saida taci sosai sannan ya tashi zai tafi "zan fita kina da bukatar wani abunne?"

Bata dago ba ta girgiza kai alamun Aa.
 "OK toh Saina dawo"

Da ker ta danne zuciyarta tace dashi  "am dama inasan magana dakai ne"


Yayi mamaki sosai sannan ya dawo ya zauna yana kallanta.

Shiru kuma tayi dan zuciyarta na wasisaan gayama,ga kunya datake ji,gashi tana tsoran karya gwaletah.

 Har saida ya kosa da zaman yace da ita "ina jinki fah" ya fada yana duba lokaci.

"Ah mh dama,dama zance makane hm inasan raba girki" ji take kamar ta nutse kasa dan tsabar kunya wani irin taji,saida ta fada take danasani.

Shiru yayi yana kallan yanda hankali ya tashi yana Murmushi dan yasan gaya mata akai  ba zabin ranta bane.
Amma duk da hakan yaji dadi sosai.

"Uhmm shikenan babu damuwa inna dawo zamuyi magana amma kafin nan ina fone inki?"

Mikewa tayi itama abun ya bata dariya sannan ta dauko ta kawo mai.

Amsa yayi yasa mata numb.ya kira tashi ta shigo wayar sa sannan ya mika matah.

Tashi yayi ya fita daga dakin.

Kamar tamai adawo lafiya kuma saita fasa.


Kallo numb.ta tsaya tana tunanin sunan daza ta sakamai kawai ta saka ya Fahad tayi saving ta ajje wayar ta gyara wajan ta nufi toilet danyin wanka.


*★★*
Yawwama tunda Fahad ya fita take tsaye bakin window harya fito.
  Kamar tayi me takeji dan ta kulu iya kuluwa.
  Tabbas sai nayi maganin wannan er iskar yarinyar me kama da aljannu fuska kamar ta er bby amma harta iya soyayya.

Tsaki taja tabar wajan.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Gida ya nufa dan ya gaida su Dad.

Yana isa me gadi ya bude masa ya shiga yayi parking motarsa sannan ya shiga gidan.

Da sallama ya shiga falon.

Mum da Aisha ne zaune suke kallo.

Tare suka amsa masa da Murmushi a fuskarsa.

Zama yayi tare da gaida su.

Amsawa sukayi,amma Mum ciki ciki dan haryanzu tana jin haushin shi.

"Ya ina Amarya?"fada tana Murmushi.

" tana nan lafiya qlau,ke me kike har yau baki tafi gida bah"

"Yau zan tafi dan Allah ka kawota ta yini pls yaya"

"Ohk insha Allah  zan kawo tah"

Mum tana jinsu bata sa baki bah,amma taji ddin yanda yake nuna kulawa akanta.


"Mum Dad baya nan ne?"

"Jiya ya tafi kaduna sai Mon.zai dawo"

"Ohk Allah dawo dashi qalu ,Cwt Mum naga kamar haryanzu naga ana fishi dani" ya fada yana dariya.

Murmushi itama tayi tare da kauda kanta.

"Wallahi Mum ayi hakuri air bansan haka er taki take bah😹"

"Fahad tashi kaban waje" Mum ta fada,
Aisha kuwa ba'a abunda take banda😹.

"Toh anyafemun"

"Allah yaba Ku zaman lafiya da zuri'a me albarka"

Ameen duk suka amsa.

Sannan ya mike " ni bara na shiga cikin gari ke ki gaida megida naki "ya fada ma Aisha.

Sannan ya fita daga gidan....






😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer*😘[24/3 23:30] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳       ⚜        🌳🌳
🌳                              🌳
              👑👑
                 🌳
    *MARAICHI*❣
              *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
    *(Zeenaseer😘)*




7⃣1⃣





*••••••••••••*Misalin karfe *2pm* Sapna ta kira Zee awaya.
Tare da rokwanta kan dan Allah ta taimaka tazo.
   Nan ta yarda tare da fadin tana zuwa.


*★★*
Yinin ranar haka Salma ta yini,babu walwala ko wanka ta kasayi dan bakin ciki bare gyaran gida.
   Daga nan ta koma can ta rasa abunda ke mata dadi har zazzabin dole yake neman kamata. Dan tsabar kishi.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Kamal ne da Bash zaune a wani gidan gona suna hira.

Bash ne ya dubi Kamal tare da da fadin "kai wai kuwa kwana biyun nan lafiyarka qlau kuwa naga duk ka canza"

Tsaki yaja tare da fadin "Wallahi yarinyar nan ke neman haukatani"

"Wace yarinyar kenan?" Bash ya tambayeshi.

"Wallahi tunanin wannan Sapna ke hanani sakat,na rasa yanda zanyi na yaceta cikin xuciyata amma abun ya faskara"

"Lallai guy kana da aiki babba atare dakai,kasan saide mu hakura da kaima Leon itah"

"Bash kenan kai ta zancan Leon ma kamar,ae Wallahi ni yanzu ba wanda ya isa yasa na kaima Sapna Leon,kasan yanda nakeji kuwa akanta,auranta ma nakesan nayi Wallahi kaga saimu bar kasar gaba daya mah"

"Kutt gaskiya inaga ka fara tabuwa kamal'yarinyr da take da aure zaka aura kuma kanwar matarka"

"Toh saime aciki,kaga Malam nasan kanasan Safiya ni dama ba santa nake bah,na samu abunda nake nema awajanta kai nama saketa kuma Wallahi me rabani da Sapna sai Allah" yana kaiwa nan ya tashi yabar wajan mah.

Binshi Bash yayi tare da fashewa da dariya dan gani yake makar ya fara tabuwa.
   Kiran Safiya ne ya shigo cikin wayarsa.

Murmushi yayi tare da dagawa" saurauniyar mata kina inane"

Daga can bangaran kuma tace "ina gidanka tun dazu naxo kuma bakanan"

"OK pls ganin zuwa "

Sannan ya katse wayar ya tashi ya shiga motarsa shima ya tafi.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
   Zee da Sapna ne zaune afalon Sapna suna hira.

"Sapna nifa tafiya zanyi wlh yamma fah nayi"

"Haba dan Allah kamar ana mintsininki bafa ki wani dade bah"

"Hakane amma sai mijinki ya dawo inan"

"Ke Wallahi baya dawowa da huri ki bari in Anyi magriba basai kitafi bah"

"Magribah! So kike ahani zuwa gidan ki gaba daya kenan"

"Toh yanzu naji kuma na gode da shawar warin da kika bani,amma kamar da huya nayi amsani da kayan nan na English wear na cikin akwatunan nan"

Dariya Zee tayi "Wallahi sappy baki da kaii,karki saka mana ni me ruwana,mijinki fah zakima kwalliya ba Zee bah.

" Nasami ai ni Wallahi kunya nake ji"

"Ohk! Very soon zaki dena jin kunyar nan muna nan dake"

Mikewa tayi tare da rataya jikarta "kinga inna biye miki Wallahi sainakai magribar gwara na tafi sai kuma wani tym din"

"Toh jarababba ina zuwa kamar zan cinyi ke" ta fada tare da shiga dakin,
Kayan makeup ta zubo mata a Leda sannan ta saka hijab dinta ta rakata har bakin gate sukayi sallama ta tafi.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
Bakuwace zaune saman kujera cikin falon gidan su Maryam *(Maman su Sapna)* Gabanta kayan ciye ciyene da shaye shaye.

Bayan sun gaisa da dattijuwar matar wanda ita ce Hajiya kakar su Sapna.

"Hajiya kamar yanda na taba muku bayani a baya ni sabuwar likitace a asibitin mahaukata na dawo aikine nan.
   Wato gaskiya hajiya na duba haukan Mayam anya bakya ganin sammu aka mata kuwa"

Shiru Hajiya tayi tana saurarn tah.kafin tace "Likita kwanakin baya 3mnths dasuka huce tabbas akwai wani Likita Namiji daya kawo mana irin wannan amma sai Babanta yaki yarda haka aka bar zancan shine nake ganin koda kuwa an sanar dashi yanzun ba lallai bane ya amince"

Shiru tayi nadan lokaci sannan tace "Gaskiya ina tausaya mata,Wallahi hajiya duk bincikan da zanyi na gano kwakwalwarta qlau take bata da matsala kinsan rayuwa hajiya ki yarda Asiri aka yima er ki.
  Ni gaskiya tsakani da Allah taimakon Ku zanyi,zan dauki Maryam daga asibiti na maidata gidana zansa arinka mata addu'a ko Allah zaisa a dace,amma karki sanar dame gidan naki"

"Gaskiya Dr.naji dadi sosai kuma Nagode mutukar gaske ko nawa kike bukata insha Allah zan biya"

"Uhmm hajiya kenan sabo da Allah zanyi,dukkan ciwan ya mace na ya macene,kodan me gidanta da kuma yarntah,ko bata dasu ?"

Shiru Hajiya tayi tare da fadin"wato Likita tabbas Asiri akayima maryama hardamu kanmu domin Wallahi babu wanda ke kula ma da yaranta,dan megidanta Allah yayi mai rasuwa gashi kuma yaran suna can gidnsu"

"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un tabbas Allah bazaibar azzalumi ba akallah zatayi 10 yrs kenan da wannan cuta kuma gashi yaranma abun tausayi,Hajiya ki godewa Allah sannan ki tashi tsaye da addu'a kuma ki nemo jikokinki tun kafin rayuwarsu ta lalace.
Nima ina aure anan garin ina da yara uku maza biyu sai mace daya yanzu na farkon yayi aure na biyun kuma yana karu sai kuma ta ukun Aura Zainab"

"Allah sarki Allah ya raya kuma biya ki kan taimakon da kike insha Allah zamu yi kokari da addu'a Allah ya bata lafiya kuma mu dauko mata yaranta"

" yawwa hajiya nizan tafi sai kuma kinjini,hannun ta sanya a cikin jaka ta dauko dan karamin Card,
"Gashi wannan address din gida nane da kuma numb.wayata"

Godiya hajiya taita mata sannan ta rakota ta tafi.

Ita kanta Hajiya kanta ya gama daurewa,ina Sapna da Shaheeda?

 👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑

*Katsina*

Yaune ranar da Aunty Ummie ki shiryama Shaheeda walimar na shiga *Ss1*.
  Kawayanta cike da gidan sunta shagali.

Sanye take da dohuwar riga peach ta gyara gashinta tasha lalle tayi kyau sosai kamarsu daya da Sapna dande Sapna ta fita hanji ita kuma tafi Sapna haske.
   Tayi kyau dama tana da dan jiki ba kamar Sapna bah.

Sai faman hotona ake dauka sai dariya take tana murna.

Shaheeda najin dadi sosai dan bata rasa komai ba duk abunda take bukata shi Aunty Ummie ke mata.

Kuma tana zuwa gidan Khadija tadan matah Hutu.
  Amma haryau har gobe taki mantawa da Sapna duk lokacin data tunata saitayi kuka.
   Shaheeda Nada tsiwa da fada ba kamar Sapna dake salihaba,inba kuleta akayiba bata fada.

Kullum burinta da addu'a ya taga Sapna.
Kuma suna waya sosai da Aunty Rahma dan itama yanzu ta tuba ta zama mutuniyar azziki dan harta haifi danta *Ibrahim* suna kiransa da *Daddy* yanzu zaiyi shekara biyu.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑

*Kebbi*

Jama'a cike gidan su Husnah *( kawar Sapna)* Ana bikintah.

Mutane anata shagali da yake ranar ne huni.
Duk sun sha anko sunyi kyau dawo.

Zaune na hango Aunty Rahma tana cin abinci.
  Daddy na gefanta yana wasa,itama sanye take da Anko din.

Amaryama tayi kyau tana tsakiyar filin rawa su Fiyyah, jiddah,Ashemi da Bellza sunta faman tika rawa,su Mhizdijah, ummcy, Ummie Khaleel sune masu liki,Ummiejay da Daneji an zage anata loma abinci baji ba gani😜.

Biki yayi dadi sai kuma yamma aka nufi kai Amarya.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Ban garan Umma kuwa,anata faman Business dan Safiya na aiko mata kaya tana saidaw,an kara gyara gidan gwanin kyau.
   Kullum cike yake da mutane maza da mata.
Ta kuma gogewa ta canza sai cin duniyarta take da tsinke.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑

*Bauchi*

Salma tana kwance a falo bayan ishsha tana faman tunani saka mahaukaciya kanta ba dankwali,gashin duk ya hargitse.

Da sallama ya shigo ya nemi waje ya zauna.

Kallanta yayi "Uwar gida hutawa akeyine"

Banza tayi dashi,dan haushi yake bata.

"Ki tashi zaune inasan zamuyi magana" ya fada yana kallan tah.

Ko motsawa batayibah balle ta bashi amsa.

Wayar shi ya Ciro daga aljihu tare da dialing numb.Sapna wanda yayi saving da soulmate.

*★★*
Tana kwance kan gado bayan ta idar da sallar ishsha ko hijab din bata cire bah,

Kirane ya shigo wayar tata.

Ganin wanda ke kiranne yasa tayi mamaki sannan ta daga.
Tare da sallama.

Bayan ya amsane yace da ita tazo part din Salma yana san ganinta.


Mikewa tayi tare da gyara hijab din ta kara feshe jikinta da turare.
Sannan ta sanya takalmin ta tajanyo kofar ta nufi part  en Salma.


*★★*
Jin yana wayane tagane da Sapna yake da sauri ta mike zaune tana kallansa.

Shima kota kanta baibibah yaci gaba da danna fone dinsa.



Ahankali ta turo kofar dakin tare da sallama.

Da sauri Salma ta kalleta tare da wurga mata harara...





😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer😘*
[24/3 23:30] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
     *MARAICHI*❣
               *NA*
  *Zainab Naseer Sarki*
       *(Zeenaseer😘)*




7⃣2⃣


*Ga username dina pls ga masu following ko voting ina a wattpad*
   *#zeenaseer908*
*Lov u oll😘😍❤*






⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
*•••••••••••* Ba tare da Sapna ta tanka mata bah ta karaso cikin Falon tare da zama saman carpet din falon.
   Kanta a kasa ahankali ta furta "Aunty ina yini"

Salma kamar ta rufeta da duka taji,amma sai tayi banza da ita kamar bama da ita take bah.

Cikin haushi ta kalli Fahad tare da fadin "in banda ka rainamin hankali akanme zaka kira min wannan yarinyar cikin dakina ubanme zata yimin" tana magana tana nuna Sapna

Sapna da tun shigowar ta kanta a kasa bata tanka mata bah.

Kallan ta yayi "magana zamuyi kuma Nina kirata ba ke bah sabo da haka ki bari na gama fadin abunda zan fada kiga in zata zauna anan din"

Shiru tayi batare da tayi magana bah tana jiran me zai fada.

"Amma Salma kece babbah sabo da haka inasan ki rike girmanki kamar yanada Sapna take karama zata tsaya a matsayinta,sannan Ku Sani gaba dayanku a karkashina kuke,bance Wata taci zarafin Wata bah,za'a raba girki ko wacce zata rinka kwana biyu,gobe insha Allah zan koma dakin Sapna nayi mata kwana biyun tah,duk da......."

"Dakatah! Fahad" Salma ta fata tare da mikewa tsaye,
"Wallahi baka isaba tayama zaka ce nayi sharing miji da wannan kucaka,jaka,mahaukaciyar tsintacciyar magen wlh it can be possible"

"Salma karda ki kuma kiranta da irin wadan nan bakaken kalmomin" shima ya fada cikin bacin rai tare da mikewa tsaye.

Itade tana zaune kamar wanda ruwa ya cinye amma maganganun Salma na bata mata rai ainun.

Murmushi takaici Salma tayi tare da kallan Fahad din kasa da sama sannan ta matso gaf da fuskarsa cikin tsiwa
 "kaban kunya Fahad, wallahi kai ba karamin munafiki bane"

Tassss! Ya kwasheta da mari, "Ni kike gayawa wannan maganar ni kike ciwa munafuki sabo da baki da hankali"

"Fahad nika Mara sabo da wannan shegiyar yarinyar"

Tsaye Sapna ta mike tare da fadin "karki kuma cemun shegiya sabo da ni yar sunace dan aure ya hadani dake bazan tsaya kina aibatani ba san ranki,kuma da kike maganar bani da ilimi akwai babban jaki dazai nuna mijinshi ya zageshi,Wallahi baki caccanci zaman aure bah saboda bakisan darajar shiba"

Mamakine ya hanasu yin magana gaba dayansu,musamman Salma dake rike da kumatunta dayasha mari.

"Kekin isa kizo har cikin dakina kimin rashin kunya"

"Wannan kuma matsalar kice sannan ta juya ta kalli Fahad tare da fadin Hubby zan iya tafiya?

Shikuwa daya koma kamar an dashi a wajan yana kallan Sapna data kasheshi da mamaki baki bude " am mhh zaki iya saida safe"

Juyawa tayi zata fita tare da fadin "Saida safe Aunty"

Kukan kura tayi tare da janyota baya ta hau dukanta.

Da ker Fahad ya babbareta daga jikin Sapna shima saida ta bigeshi janta yayi cikin dakinsa ya kulle da key sannan ya dawo falon.

Taimaka mata yayi ta tashi tare da gyara hijab dinta.
   "Sannu kinji babu inda yake miki ciwo?"

Murmushi ta sakar masa "babu komai karka damu saida safe"

Juyawa tayi dan tafiya ta kasa dan ta Dakar mata kafarta da karfi saura kadan ta fadi.

Da sauri ya kamata tare da daukarta cak.

"Sannu kinji nasan dama dole wani wajan yayi ciwo bari na dauko key na kaiki asibiti"

"Aa basai ka kaini ba,zan ji ddi kakaini dakina"

Ba musu ya nufi part dinta da ita,sannan ya bude,har kan gadonta ya kaita sannan ya tube mata hijab din,ya gyara mata kwanciyar tatah.

Sai faman kallan shi da kuma tausayin sa daya kamata,nan danan taji kishin Salma ya taso mata.

"Kina da bukatar wani abunne in dauko miki?" Ya fada yana kallanta.

"Bana bukatar komai" itama ta bashi amsa tana gyara blanket din daya rufeta dashi.

"Gud nyt" ya furta tare da bata peck a goshi sannan ya juya ya fita daga dakin tare da rage mata hasken fitilar sannan ya kulle mata kofar.

Lumshe idanunta tayi dan bataso ya tafiba,tasan yanzu zaije ya lallaba wannan matar jarabbah.
Tsaki taja "Toni mene mah abun damuwa" sannan ta kuma gyara kwanciyar tah.


*★★*
Shima a dan yaso bah ya tafi yabarta,saida ya jima abakin kofar sannan ya tafi.

Yana shigowa dakinsa ya nufah ya sa key ya bude.

Tana zaune bakin gado,ta hada kai da gwiwa sai faman kuka take tayi sharkaf da gumi duk ta fita hayyacinta.

Kara sowa wajanta yayi tare dasa hannu zai tabata.

Da sauri ta mike tsaye tare da fita daga cikin dakin.

Hannun sa yasa tare da shafa kansa da fuskarsa sannan ya furzar da Wata iska daga cikin dakinsa ya mike dan bintah.

*★★*
Tana shiga dakinta key ta saka sannan ta kama hauka ta janyo wancan ta zubar da wancan ta durkushe a tsakiyar dakin tare da fashewa da wani saban kukan.



Yana kara sowa jikin kofar ya rinka kiranta yana rokwanta ta bude amma ta yimasa banza banda kuka ba abunda take.

Daya gaji ya koma dakinsa,shima ya jima beyi bccinba sannan ya kwanta.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Koda Fahad ya tashi sallar asbah alwala yayi ya nufi massallaci,bayan ya dawo gida harya shiga daki sai kuma ya fito ya nufi part din Sapna.


*★★*
Ko da itama ta farka zatayi sallah kafar tata tayi tsami kasa takata tayi ga wani azaba da take mata.
   Zama tayi bakin gadan tana kallan kafar tana kuka.


Da sallama ya turo kofar dakin,tare da kunna fitilar me haske.

Ido biyu sukayi da ita tana shafa kafar tatah.

Da sauri ya karaso wajan nata,tare da durkusawa tare da kamo kafar ya Dora kan ciyarsa sannan yakai hannun yataba inda yaga tadan kubura yayi jaa.

 " *auchh!*" tadanyi kara tare da dafa kafadarsa ta janye kafar.

Rike kafar yayi yana kallanta "sannu,kinyi sallah ne?" Ya fada yana kallanta.

Gigiza mai kaitayi alamun "Aa"

"Toh kije kiyi sallah bara sai muje asibiti su duba kafar taki"
Sannan ya mike,har yakai bakin kofa

Ahankali ta furta "Nifa bazan iya tafiya da kafar bah"

Juyowa yayi ya karaso har inda take sannan ya durkusa ya dauko ta ya nufi toilet din da itah.

Zaunar da ita yayi kan baths din sannan ya juya ya fita ya tsaya kofar  toilet din..

Murmushi tayi sannan tayi tsarki tayi alwala.

Rasa me zatace tayi danya shigo ya dauketa.
"Yaya nagama " ta fada.

Shima kansa taso ta bashi dariya.
   Already ya shimfida mata abun sallah.

Shiga yayi ya daukota sannan ya saka mata hijab din ya fita daga dakin.

Yana fita ta tayar da sallah.


*★★*
Part din Salma ya nufa ya shiga daki ya dauko key dinsa tukun ya fito daga dakin har lokacin bata bude dakin bah.


Lokacin daya koma ta idar da sallah, daukarta yayi ya nufi cikin motar da itah.
   Bayan ya ajjetane ya zafayo ya shiga side din driver sannan ya kunna me gadi ya bude gate suka nufi asibitin.


Bayan sunje Anyi duk abunda ya dace sai wajan *7am* sannan suka dawo.

Lokacin da suka iso bacci take daki ya kaita ya kwantar sannan ya fito ya koma part dinsu.

Shima komawa yayi dan baccin be ishe shibah.



👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
Yau Hajiya da huri ta dan ita hankalinta ya dawo jikinta.
  Driver ta dauka kasancewar Alhajin ya tafi Umrah ta nufi kebbi dan dauko jikokinta.



*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Lokacin da Dr.ta dauko Maryam daga asibiti batare da Sanin kowa bah,dan ba'a bari a can asibitin.
   Daki daya ta ware mata, kuma Alhmdullh tun jiya da aka mata karatu bata yi wani doke doke bah,bacci ta samu sai yanzu data farka da safe.

Zainab data fito dan shiga kitchen taga Maryam din atsaye abakin kofa dan tamaji tsoro.

Murmushi ta sakar mata tare da fadin "ina kwana"

Itade kallan ta kawai take ...







😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer😘*
[24/3 23:30] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳         ⚜      🌳🌳
🌳                              🌳
                👑👑
                   🌳
      *MARAICHI*❣
               *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
     *(Zeenaseer😘)*




7⃣3⃣




*•••••••••••*Ganin tana tsaye bata da niyar tafiya ga kallan da take ta faman yima Zainab din yasa ta kamata,ta kaita ta zaunar da ita saman sofa,sannan ta nufi dakin Maman tasu.

Da sallama ta tura kofar tare da shiga.

Tana kwance saman gadon tah.

Karasawa tayi tare da zama gefenta.
Ahankali ta fara kiran sunan tah "mama! Mamah!!"

"Zainab ki rabu dani mana na huta menene kuma?" Maman ta tambayeta cike da kosa wah.

"Toh mama patient dinki ce ta tashi gata can a falo"

Da sauri ta mike zaune tare da fadin "da gaske"
Nan danan ta sauko daga kan gadan nata,ta fito falon.

Zaune taga Maryam din tana ta faman kalle kalle acikin falon.

Zama tayi kusa da itah,tare da dafata.

Itade Maryam bata da aiki sai kallan mutane.

Itama Zainab tana tsaye tana kallan Maryam din dan tana bata tausayi.

Maman ce ta kalli Zainab tare da fadin "Zainabu hado mata tea muga ko zata sha amma madara kadai zaki saka"

"Toh Mama ta fada tare da yin hangar kitchen din"

Kallan ta Dr.Hussainah tayi tare da fadin "Maryam!"

Amma shiru babu amsa kamar mah bada itah take bah.

Shiru Dr.tayi tare da fadin "Allah Nagode maka Allah ka karama matar nan lafiya kasa ta dawo haiyacinta Ameen"

Lokacin ne Zainab ta shigo da cup din tea a hannun ta sannan ta mikama Maman tatah.

Amsa tayi tare da kamo hannun Maryam ta saka mata "Maza kisha" ta fada tana nuna matah yanda zatayi.

Ahankali takai bakinta tana kallan su,har saida ta shanye duka sannan Dr.ta amshi kofin.

"Yawwa Zainabu kinga kuwa ta shanye bara naje nayi mata wanka saita kuma jin dadin jikin nata ta kara hutawa kafin masu addu'a suzo.

Ahankali ta kamata suka nufi dakin da aka bata.

Saida Dr.tayi mata wanka tas,ta saka mata kaya masu kyau ta fesa mata turare.
 Itade sai yanada akayi da ita ba um ba um um.

Bayan ta gama shiryata ta sa Zainab ta kawo mata abinci.

Da kanta ta zauna ta bata,saida taci ta koshi tasha ruwa sannan ta kwantar da ita ta fito daga cikin dakin.


Da sauri Dr.ta dauko wayarta ta kira Hajiya.

Bayan sun gaisa take tambayarta yame jiki.

Murmushi Dr.tayi tare da fadin " Hajiya me jiki saide mu dada godema Allah dan alhmdullh jiki yafara kyau Wallahi"

Cike da farin ciki Hajiya tace "Allah ubangiji ya kara sauki kuma ya biya ki,nima yanzu muna hanyar kebbi insha Allah zamu dubo yaran"

"Toh Allah ubangiji ya dawo daku lafiya" sannan sukayi sallama.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
Sai kusan *11am* sannan Fahad ya farka,wanka yayi ya sanya kayansa ya fito ya nufi dakin Salma.
   Koda ya shiga bega kowa cikin dakin bah,saide karan ruwa da yaji cikin toilet din.

Zama yayi bakin gadan yana jiran fitowarta.

Bayan kamar 5mins da zamansa ta fito daure da towel.

Kallo daya tayi masa ta dauke kanta,ta nufi gaban mudubi dan shafa.

Murmushi yayi dan shi dariyama take bashi.

"Salma pls kafin ki shirya inasan muyi magana dake"

Banza tayi masa dan dama ta saba.

"Ohk! Naji ko baza ki dakata da abinda kike yi ba,nasan kina jini tunda kunne keji.
  Da farko de kiyi hakuri game da hannu na dana samiki amatsayin duka wanda hakan be taba faruwa a tsakanin muba shikara da shekaru,wannan ki Sani badan bana sanki bane yasa na auri Sapna bah,asalima ni bansan hakan zata faru bah.
  Kamata yayi ace kina Abu yanda ya dace,koda zakiyi kishi kiyine na hankali ba irin wanda kike yanzu bah,kuma dama ko wani namiji mijin mace4 saide in bazai iya adalci a tsakanin suba akace yayi guda daya"ta sawa yayi tare da kamo hannun tah yana kallan tah " kina ikirarin kina sona inda gaskene meyasa bazaki bani hadin kaina muyi zaman lafiya uhmm! Kinfisan muyita samun sabani,shekarar mu nawa da aure,,amma ba ma 1wk batare da rigima bah,toh yaushe hakan zaizo karshe ne yaushe ?"

Cikin kuka tace "Fahad ka fita a dakina banasan ganin ka,inshar kazo ka gayamin hakane dan kasamu hadin kan zaman lafiya ne,toh kasani Wallahi muda zaman lafiya a gidan nan har abada mundin baka sallami yarinyar nan bah"
Tana kaiwa nan ta fice daga dakin ta barshi a tsaye.

Ajjiyar zuciya ya anje sannan ya fito daga dakin,
Dakin Sapna ya nufa dan yasan tana bukatarsa.

*★★*
Tana kwance kan gadanta tana game a wayarta dan ta jima da tashi daga bacci.

Ahankali da turo kofar dakin da sallama yana Murmushi.

Tana hada Ido dashi batasan lokacin da Murmushi ya subuce mata bah itama.

Karasowa yayi tare da zama gefanta.

Ajje wayar tayi tare da fadin "ina kwana"

"Lafiya qlau ya fada,tare da fadin ya kafar er gurguwa" cikin zolaya.

Murmushi ta kumayi me sauti.
"Ya nidince gurguwa?"

"Eh mana,yanzu saiki tashi kiyi wanka"

"Toh" ta fada

"Kosai na kawo agaji tukun"

Kanta ta sauke kasa tana Murmushi.

Mikewa yayi yaje ya hada mata ruwa sannan ya dawo har lokacin tana nan inda ya barta.

Hijab din ya cire mata da dan kwalin kanta.
Ahankali ya fara zuge mata zip din rigar tata,

Da sauri ta rike hannun sa tare da fadin "Ya zan iya ka kaini toilet din"

Ba musu ya kaita ciki sannan ya ajje mata towel a gefe ya fita.

Kitchen din ya nufa dan hada masu breakfast.

Kwai ya soya musu sannan ya hada Tea fita yayi ya bama me gadi kudi ya siyo musu bread guda biyu.

Sannan ya koma.

Yana shiga dakin kofar toilet din yayi knocking tare da fadin "Kin gama?"

"Eh" tace dashi.

Shiga yayi tana zaune daure da toilet din ta rufe jikinta da rigar sai faman kunya takeji.

Daukota yayi daga ciki ya maidota dakin kangado.

Mayyufanta ya miki mata.

Gaba daya ta kasa sakewa dan kunya take mugunji.

Matsowa yayi kusa da ita "Sapna kunyata kike ji ko?" Ya tambayeta yana kallanta.

Kai ta girgiza masa alamun batajin kunyarsa.

"Uhmm! To kawo man na shafa miki"

Mika masa lotion din tayi kamar zata nutse takeji.

Amsa yayi ya zuba a hannunsa sannan ya zame towel din bayan nata ya fara shafa mata.

Gaba daya jikinta ya fara mutuwa idanta a rufe.

Saida ya shafa mata a bayanta,huyanta,hannu da kuma sauran su saida ya kama toilet din kirjinta.

Itama rikewa tayi gam taki sakar masa.

Kofar gidan sukaji kamar ana bugawa,,dakinta yayi sannan ya fita daga dakin.

Da sauri koman bata shafa ba ta lallaba ta dauko bra da pant dinta ta saka sannan ta koma kan gadan da ker dan bazata iya dauko kayan bah.

Bayan ya bude gidan ya amashi nasu bread din dayan kuma yace yakaima Salma.


Koda ya koma dakin zaune ya ganta tana duba kafar tata.

Murmushi yayi ganin ta sanya bra.

Wardrobe din ya bude dan dauko mata kaya,amma gaba daya kayan hausawane babu English wear ko daya.

Juyowa yayi ya kalleta tare da fadin ina English wear dinki.

Shiru tayi dan kunya takeji ta saka kayan nan.
"Suna can dakin" kawai ta fada.

Dakin ya nufa ya dauko mata Wata riga multi color me karamin hannun iya cinya sai karamin wando fari jeans ko gwiwa bekai bah.

Yana dawo wa dakin ya mika mata tare da fadin "ko na saka miki?"

Amsa tayi "Aa zan iya ,amma pls ka fita"

"Gaskiya ni bazan fitaba saide na juya bayana"

"Toh naji amma harda idanka zaka rufe"

Dariya yayi "toh naji"
Sannan yayi yanda take so.

Bayan ta gama sawa. Tace dashi "Nagama sakawa"


Gashinta ya gyara mata sannan ya daukota dan suyi breakfast.



👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
*6:23pm* Su Hajiya suka isa kebbi kai tsaye gidan Aunty Naja suka zarce  dama sunyi waya dan tasan da zuwansu da kuma dalilin zuwan nasu.


Suna isa gidan ana jiran sallar magariba.



Sai bayan sunci abinci sannan sukayi sallah.

Suna zaune cikin falo ita da Hajiya.

Aunty Naja ce tace "gaskiya Hajiya abun nan yana bani mamaki,danni gaba daya an daukemun tunanin yaran nan cikin raina.
  Kuma suma basa zuwa ballantana har nagansu na tuna dasu.

" Naja'atu yanzu kuma aisai addu'a kawai,insha Allah in gari ya waye sai ku je can gidan nasu mugani.

Hakane kam! Allah yshige mana gaba.

"Ameen"


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
Kamar er baby haka Fahd ya maida Sapna ita kuwa sai faman shagwaba take masa yana kara rikicewa.

Bayan ya shiyo musu abunda sukaci da daddare suna zaune a falo,yana saman kujera ita na zaune a kasa ta mike kafarta,ya mike tsaye tare da fadin
"Bara naje nayima Salma saida safe sannan ya fice"

Bataso hakan bah,sai dan bayanda ta iya aa fice daga dakin.






😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer😘*
[24/3 23:30] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳         ⚜      🌳🌳
🌳                              🌳
                👑👑
                   🌳
      *MARAICHI*❣
              *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
     *(Zeenaseer😘)*




7⃣4⃣




*•••••••••••*koda ya shiga part din nata, bata cikin falon nata,bread din daya kawo mata da abincin daya kawo mata duk suna nan ajje acikin falon.

Dakinta ya nufa da sallama ya tura kofar.

Tana kwance kan gadonta,tana danna wayar hannunta.

Karasowa yayi tare da zama gefanta.

"Salma" ya kirayi sunatah,

Naam ta amsa batare data kalli inda yake bah.

"Kina bukatar wani abunne zan kwanta sallama nazo muyi"

"Bana bukatar komai" tana fadin haka ta juyamai baya tare da gyara kwanciyarta.

Mikewa yayi tare da janyo mata kofar ya fice daga dakin.

Dakinsa ya shiga ya canza kayansa sannan ya fito ya ja mata kofar.

*★★*
Yana dawo wa part din ya kulle kofar sannan ya shiga.
   Tana zaune inda ya barta tana kallo.

Karasowa yayi tare da fadin "kin gama kallan muje mu kwanta"

"Eh" ta daga mai kanta.

Kayan kallan ya kashe sannan ya dawo ya dauketa cak! Harkan gadanta.

Gyara mata kwanciyar tah yayi,sannan ya rage hasken fitilar dakin sannan ya koma can gefe ya kwanta tare da rufewse.

Shiru kowanne ya kasa baccin acikin su, kowa da abunda yake sakawa cikin ransa.

Ahankali ya matso gareta tare da janyota kan kirjinsa ya rufesu.

Basu dau lokaciba bacci ya dauke su.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
*11am* lokacin Hajiya da Aunty Naja suka fito suka nufi gidan su Sapna.

Koda suka shiga cikin gidan part din su Umma suka nufa.

Sun jima suna sallama kafin a amsa musu.

Wata yarinyace wanda shekarunta basu huce *18* ta fito daga cikin daki tare da gaida su,

Amsawa sukayi sannan Aunty Naja tace da ita "Babu kowane agidan mukaji shiru"

"Wallahi Umma bata nan saide Na kaiku part din Aunty Rahma"
Cewar yarinyar.

Hajiya ce tace "babu damuwa muje can din"

Nan ta musu jagora har cikin Falon Rahman.

Da sallama suka shiga sannan yarinyar ta koma.

Zama sukayi kan kujera suna jiran fitowar Rahman data amsa sallamar.

Daga cikin daki ta fito hannun ta dauke da takalmi a hannunta Daddy na Binta abaya.

Da fara'a ta zaunata tare da gaidasu.

Sannan ta saka masa takalmin daya ke san asaka masa.
Daki ya ruga dan yin wasanta.

Kara gaisawa sukayi,sannan ta kalli Aunty Naja tace "Nikuwa kamar naso gane fuskar nan"

Murmushi tayi tare da fadin "ai anan unguwar nake zaki iya sanina"

"Allah sarki toh sannunku da zuwa" ta kuma fada.

Aunty Naja ce tace "Wato ni yayar Maryam ce wannan kuma mahaifiyar muce wato kakar su Sapna"

Da sauri Rahma ta kara kallanta tare da zaro idanu.
"Allah sarki" ta kara fada.

"Munzo ne dan ganin ita marikiyar tasu kuma mu dauke su dan tafiya dasu"

"Toh aiki jah"Rahma ta fada.

Nan ta shiga zaiyana musu abunda ya faru tun saka ranar bikin ta har zuwa tafiyar Shaheeda katsina zuwa lokacin.

Daga Hajiya har Aunty Najar kuka suke itama Rahmar saida tayi kwallah.

Nan de akaita basu baki sukayi shiru.

" dan Allah ko kina da numb.en can katsinar?" Aunty Naja ta tambaya.

"Eh" Rahma ta fada,sannan ta dauko ta basu numb.

Godiya sukayi sannan suka tafi.

Gaba daya sun rasa abinyi ko ina zasuga Sapna Allah masani.

Sannan suka yi sallama suka bar gidan.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Alhmdullh jikin Maryam yana sauki ba laifi kullum cikin gyarata ake da kuma bata kulawa ta musamman.

Harta fara sabawa daso dan har dan Murmushi take musu.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑

*BAYAN SATI BIYU*

Soyayya me karfi ta shiga tsakanin Fahad da Sapna dan kullum cikin faran tamata yake.

Ita kuwa Salma har kwantar ta akayi a asibiti kusan kwanan tah 4 a can sabo da tsabar kishi dake damunta harya saka mata cutah.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Kwanan Hajiya 3 a kebbi sannan ta huce katsina daga nan.
   Canma dataje sun amsheta hannu biyu biyu,kuma duk da Shaheeda bata san taba tayi murna sosai da ganin kakar tatah dan kamar tayi me dan murna.
  Kwana tah 2 a katsina sannan ta tattaro kayanta dana jikarta sukayo bauchi dan bazata iya barin taba.

Aunty Ummie haka ta hakura badan taso ba,amma Hajiya ta mata alkawarin zatana kawo tah Hutu.

Sosai sukayi kukan rabuwa.

Bayan sun dawo Bauchi murna sosai wajan  Shaheeda nan aka naima mata makaranta mekyau da tsada aka sakata.

Sosai Hajiya ke Nuna matagata,


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Yau Sapna keda girki dan haka da huri ta tashi dan yima Fahad kirki bayan la'asr.
   Tana kitchen taji kara bude kofa.

Fitowa tayi daga falon dan ganin me shigowar.

Salma ce ta shigo tare da kawarta Hasina.

Cike da Murmushi Sapna ta karaso wajan ta tare da fadin "Sannunku da zuwa Ku shigo mana" ta karashe maganar tana nuna musu kujera"

Kallan juna sukayi sannan suka shiga cikin falon suka zauna.

Kitchen ta koma ta zubo musu kayan motsa baki a tray ta kawo musu.

Sannan ta juya zata zauna.

Taratsatsa TSA....gaba daya suka zube a kasa.

A firgice Sapna ta juyo dan ganin abunda ke faruwa.

Salma ce tsaye ta rike hannu Akugu tana kallan Sapna.

Gaba daya ta zubar da abunda ta kawo musu ta bata musu gurin gaba daya.

"Haba Aunty ko bakya so ba sai kice bakya so bah amma kalli yin...."

"Dallah  ga fara ki yimin shiru,munafuka dama ance miki abinci nazo cine,wallahi kasheri nazo miki,mundun baki rabu da Fahad bah baki da zaman lafiya a gidan nan"

Murmushi tayi sannan ta shiga gyara wajan batare data tanka mata bah.
Hakan ya sanya ta kara jin haushin tah sannan suka fita daga gidan .
[24/3 23:30] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                 🌳
     *MARAICHI*❣
             *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
     *(Zeenaseer😘)*




7⃣5⃣



*•••••••••*Bayan ta gama gyara wajan kitchen ta koma dan cigaba da bunda yakeyi.


Sai wajan sallar magajere sannan ta kammala,bayan ta Jere abincan saman dining ta koma kitchen ta gyara sannan ta nufi daki danyin wanka ta shirya.


*★★*
Salma zaune cikin falonta tana waya da Safiya.

Bayan sun gama gaisawa Safiya take fada maga"Ai wallahi Salma banji dadin rashin zuwan nan nakiba ko kadan bah"

Salma ce tayi Murmushi takaici tare da fadin "Hmmm kede bari dama inasan gaya miki wani babban abun bakin ciki daya sameni"

"Gayamin Hajiya tah "

"Wallahi Fahad ne ya kara aure"

"Aure! Salma, ke kuwa kina me Zaki bari ya kara qure,Haba karki bani kunya mana Wallahi har kinsa na tsani kaina"

"Wallahi kede bari ni kunya cema ta hanani sanar dake amma tun randa kika zo din nan"

"Shegiya kawara shiyasa naga jikin ki yayi sanyi"

"Uhmm kede bari kuma dan bakiga yanda yake rawar kafa akanta bah,kamar ya maidata ciki"

Nan Safiya ta lailayo Wata uwar ashar "kuma ba matakin da ki da kika dauka,Wallahi ki zauna bakin ciki ya kashe ki"

"Hmm ranar da za'a raba mana girki nayi mata duka nasan kuma taji ciwo"

"Yo dan duka,ki batqr da shegiya kisa tabar kasarma gaba daya Wallahi kede ki jira na dawo bazan jima bah zanzo naga er iskar yarinyar ko er gdn uban waye"

"Wallahi a takaici bama asan iyayan taba er tsintuwace ta manne mai"

"Kan ubancan Wallahi sun gama dashi,er tsintuwa dan ubanta tuni ban saba mata kammatan bah,wallahi kin Matan rai,maganar bata waya bace saide na dawo"

Sannan sukayi sallama.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Shaheeda zaune cikin falo tana Assignment dan har sun sanyata makaranta me kyau da tsada.

Hajiya na saman kujera tana shan fruit.

"Hajiya" Shaheeda ta kira sunan tah.

Dago kanta tayi tare da fadin "Naam"

"Hajiya dan Allah tunda kinga gobe Friday inna dawo da huri ki kaini naga Mamatah"

"Toh Allah ya kaimu"

Murmushi tayi sannan taci gaba da rubutun tah tana tunanin yanda Maman tatah zata kasance dama Ya Sapna na nan data fi kowa farin ciki.
"Allah sarki my belovd sis ko kina ina Allah yasa kina raye cikin farin ciki" tuni kwallah ta digo kan littafin.
Sannan ta goge.


*★★*
Zaune Zainab da Maryam cikin Falo suna kallan wani film din Hausa na *BITA ZAI ZAI*suna dariya dan Alhmdullh jiki yayi kyau sosai dan harta fara tuna baya dan har saida ta tambayi yaranta kuma tana ganewa sosai har sallah tanayi.

Da yake Zainab Aunty take kiranta tace "Aunty da alama film din yana miki kyau naga kinata dariya"

"Wallahi kuwa Zainabu bakiga yanda suke shakiyanci bah da Allah dubi wannan wadah haka"

Dariya Zainab ta kuma yi cikin zuciyar kuwa fadi take "oh Allah me halittah kalli matar nan kamarsu daya da Sappy kamar Maman tah"
Kullum abunda take fada kenan.
   Kawai sai taji tana san kiran Sapna dan taji muryartah kwana biyu kuma tana san yi matah zancan makarantah.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Bayan ta fito daga toilet tana zaune kan Stoll kusa da mirror tana kwalliya wayarta tayi kara.

Mikewa tayi tana Murmushi ganin wanda yake kiran nata, loudspeaker ta bude sannan ta ajjeta kan mirror taci gaba da kwalliayr suna magana.
Bayan sun gaisa Zee tace "kwana biyu an mantah damu anacan ana soyayya"

"Hmmm! Kin fara ko,baki da dama ya gida dasu Maman"

"Wallahi lafiya qlau,intaso nazo Allah beyi bah"

"Hmm ai baki da mutunci nikuwa ina fara fita zanzo na gaida Maman insha Allah"

"Toh Allah ya kawoki"

"Ameen, mutuniyar tunda kika kiarani wallahi nakejin dadi kamar anman kyautah"

"Hhhhhh! Kede ba wani mijinki kike tunawa"
Nan suka kwashe da dariya gaba dayansu.

Nan dai sukayi sallama sannan ta sanya kayanta.

Riga da skirt na atamfa ta sanya,da dankunne da bangles tayi kyau sosai ta feshe jikinta da turare sannan ta saka hijab dinta tayi sallar ishsha dan taji an fara kira,"toh lafiya har yanzu be dawo bah"
Ta fada sannan ta tada sallah.


Bata jima da tayar waba shima ya shigo dakin sanye da doguwar jallabiya fara tas tayi masa kyau sai kamshi yake.
Da alama ya jima da dawo wa dan yayi wanka.

Ganin tana sallah ne yasa shima ya fitah.



Lokacin data idar be dawo ba dan haka ta fita daga dakin takoma falon.

Zamantah keda huya ya turo kofar falon da sallama.

Amsawa tayi tare da gyara zamantah.

Zama yayi kan kujerar tare da fadin "Sannu da zuwa ashe kama jima da dawo wa?"

"Wallahi dana shigo kina wanka shiyasa nima na shiga ciki,ataimako yinwa fah nakeji"

Murmushi tayi sannan ta mike tare da fadin "toh babban yaya"

Janyota yayi tana zuwa hucewa ta fada jikinsa ya kwantar da ita kan kujera yayi mata rumfa tare da fadin "me kika ce,maimaitah naji"

Dariya ta danyi tare davfadin "awwh! Yakuri dan Allah Hubby"

"Inna Kara jin yayan nan nidake ne" ya lakace matah hanci tare da dagata.


Dining suka nufa nan tayi serving dinsa,sunaci suna hira saida yaci abincin sosai ya koshi sannan ya tashi.

Bayan ta kwashe kayan wajan itama ta dawo falon tym din yana waya.

Nuna mata gefansa yayi alamun tazo ta zauna, Murmushi tayi tare da dage kafadarta daya alamun bazata zo bah.

Shima Murmushi yayi tare da gyada kansa alamun zai ka matah.


Koda ya gama be mata magana ba cigaba da kallansa yayi kafin ya mike.

Tana ganin haka ta rugu tana kukan shagwaba.

Dariya ma abun yaso bashi yanda ta ruga din.


Part din Salma ya nufa dan yimata saida safe.


Yana shiga ya sameta zaune a falo daga ita sai Wata er karamar Riga me karamin hannu ko cinya bata rufebah.

Zama yayi tare da fadin "Uwar gida Rangidah"

Murmushi kawai tayi taci gaba da kallantah.

Toh kina da bukatar wani abunne inajin bacci danyau na gaji inasan na kwanta da huri dan ba lallai gobe naje office bah"

Tasowa tayi daga inda take tana wani lumshe idanu tare da kwanciya ajikinsa "Bby kai nake bukata pls"

"Salma enough pls banasan rigima kinsan yau sarai ba girkinki bane"

Kamar bataji abunda ya fada ba taci gaba da romancing dinsa.

Shima beye mata yayi tare da kwantar da ita bisa sofa dake cikin dakin.

Sun jima ahakan kafin yakai hannunsa ga pant dinta ji ya taba pat ne yayi saurin janye jikinsa.

"Salma kanki qlau kuwa kina period kuma zakice kina bukatah tah"

Banza tayi a zuciya tah kuwa fadi take "kawai danna bata maka rai matarka taji haushi"

Tasowa tayi tare da fadin Haba bby toh wani abunne dan ba girkina bane.

Tsaki yayi tare da barin dakin.
Kwashewa tayi da dariya tare da fadin kadanma kuka fara gani.


*★★*
Sapna harta yi brush da alwala ta canza kaya ta kwanta amma shiru be dawo bah.

Kawai ji tayi kishi ya kamata nan ta fara kuka wiwi.
Ta jima tana kuka sannan taji karan kulle kofar alamun shigowarsa kenan.

Da sauri ta goge hawanyan tare da gyara kwanciya ta kudun dune.


Yana shigowa cikin dakin ya kulle kofar sannan ya fada kan gadan tare da janyota jikinsa.

Kwacewa tayi ta koma gefe.

Murmushi yayi sannan ya matsa  kusa da kunnan ta tare da fadin "am srry pls Soulmate zo muyi sallah"

Bata ko kalle shiba ta mike ta sanya hijab dinta,sannan ta tsaya a bayansa.

Murmushi ya kumayi ganin fushin da take harda guntun hawayanta.



Bayan sun idar da sallar ya dafa kanta yayi mata addu'a ,yana gamawa ta cire hijab din dama vest ce jikinta da wani karamin wando iya gwiwa.
Komawa kan gadan tayi tayi kwanciyarta.


Shima jallabiyar ya cire daga shi sai gajeran wando da singlet jikinsa sannan ya kwanta abayanata.

"Soulmate har yanzu fishin kike dani pls kiyi hakuri dan Allah" ya fada yana kara matseta jikinsa.

Shiru tayi idanta arufe.

Kissing kunnanta ya farayi kafin ya juyota ya hada bakinsa da natah.

Romancing dintah Fahad keta famanyi gaba daya ya kashemata jikinta,nan ta fara kuka jikinta na rawa.

Hankali be gama tashiba saida taga ya rabata da kayan jikinta.

Shima kansa rudewa yayi ganin yanda Sapna daya raina yake,gaba daya ya gama fitah hayyacinsa tamkar maye haka ya koma ko ina ya samu tsota yake.
  Ganin bazan iya kallo ba yasa na fito daga dakin.

Da sauri nafito na zauna a falo kafin na mike dan Barin gidan gaba daya.

Jin ihun da Sapna ta kwala yasa ni komawa dakin da gudu.

Ihu Sapna ke faman yi tana neman taimako,duk sunan dayazo bakinta furta wa take,tana rokwan sa daya yi hakuri,Wallahi ta hakura ta daina fishi dashi.

Amma gaba daya Fahad bemasan tana yiba,sabo da shima besan inda yake ba besan Wata duniyar yake cikiba,ya tabbata kota kusa da ita be taba jiftawa bah.

Tsawan lokaci ana Abu daya kafin ya koma gefe yana maida numfashi,cizo da yakushi babu wanda Sapna bata mai bah,

Ko motsi bata iyawa,kuka harda majina tashasu sai ajjiyar zuciya take.

Bayan ya fara dawowa daidaine ya sanya ya rungumetah gaba daya jikinsa karkarwa yake.

Fashewa Fahad yayi da kuka kamar karamin yaro saida yayi me isar sa,sannan ya saka dakinsa daidai kunnan tah yana mata addu'a.

"Lallai duk wanda tayima iyayansa biyayya yana tare da masara,babu abunda zaice sai Allah ya biya,sannan ya shiga yima Allah godiya daya bashi matar datafi ta kowa wato Sapna,Allah ka bamu zuri'a ta gari,Nagode Soulmate da wannan babbr kyauta da kiramin insha Allah zan baki farinciki da baki taba tunanin zaki shameshi koda zaiyi sanadiyar raina Nagode"

Har lokacin yana hawaye.

Ita kuwa tuni tayi baccin wahala duk abun kuka da hawaye ya manne mata a fuskarsa.

Fahad kuwa babu alamun bacci ko kadan atare dashi ya matseta ajikinsa kamar wani zai kwace masa itah har lokacin albarka yake shi matah..






😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer*😘
[24/3 23:30] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳       ⚜        🌳🌳
🌳                              🌳
              👑👑
                 🌳
     *MARAICHI*❣
            *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
      *(Zeenaseer😘)*




7⃣6⃣




*•••••••••••* Har aka kira sallah asbah amma Fahad be rutsaba yana ta faman gadi.


Mikewa yayi ya shiga toilet yayi sanka sannan ya dauro alwala,
Koda ya fito gyara mata kwanciyar yayi sannan ya fita masallaci.


Allah Allah yake a idar da sallar ya dawo gida dan gani yake kamar zata tashi ta nemi wani abun.
   Amma harya dawo bata tashiba.

Zama ya kumayi ya sata agaba yana kallo har gari ya fara haske sannan ta fara mutsi kafin ta bude idanunta ahankali da suka kymbura sabo da kuka.

Tana hada Ido dashi tayi saurin rufewa sannan ta kuma fashewa da kuka dan har yanzu zafi takeji.

Da sauri ya matsa wajanta yana me tausaya mata kamar yayi kuka.

"Sannu Soulmate Nagode kinji Allah ubangiji ta miki albarka ya bamu yara na gari"

Itade babu abunda take sai kuka.
  Fahad kamar yagi hauka dan baya san jin kukan nan ko kadan,lallashinta yake ta faman yi shima kamar yayi kukan.

Da ker tayi shiru sannan ya tashi yaje ya hada mata ruwan zafi.

Koda ya dawo dan kaita ta gasa jikinta tayi wanka kiyawa tayi.

Cikin muryar kuka tace dashi "Wallahi ni karka tabani da kaina zan tashi kuma ka fitar mun a dakina " duk idanta a rufe yake take wannan maganar.

"Pls karkice haka nasan bazaki iyaba Wallahi babu abunda zan miki pls kiyi hakuri"

Banza tayi dashi sannan ta fara kokarin Jan zanin gadan ta kara rufe jikinta,kokarin tashi ta shiga yi amma taji ta kasa.

Kara fashewa tayi da wani saban kukan.

"Ohhhh haba  dan Allah kiyi shiru mana pls Soulmate so kike nima nayi kukan ko? Haka kiko ne" yana maganar yana kallanta.

Mikewa yayi ya dauketa tana kukan da ihunta,be dire taba ko ina sai cikin baths din.

Saban ihu ta kara jin ya saka cikin ruwan zafi,tuni tayo sama tare da Dane shi.

"Wayyo Allah yaya dan Allah kayi hakuri karka kasheni wayyo Allah Mamatah ki zo zai kashni"

Haka ya turata har jikinta ya saba da ruwan kuma ta fara jin dadin.

Sai kuma ta sakeshi ta fara jin kunya tana kare jikinta da hannunta.

Cikin muryar shagwaba tace "Toh ka fita ni"

Murmushi ya danyi sannan ya fita ya tsaya kofar ban dakin yana kiranta.

Koda ya fita wani hawayan ne ya shiga bin kuma tunta ahankali ta furta "mugu kawai Allah zai sakamin"

Wankan tsarki tayi sannan tayi na sabulu bayan ta gama tayi alwala.

Ahankali ta mike tare da daura towel ta fito tana tafiya ahankali.

Yana ganin ta fito yayi maza ya kama mata hannu.

Da sauri ta kwace cikin kuka ta fara fadin "Wallahi nika kyaleni bana so"

Da sauri ya koma gefe"OK am srry pls sannu zauna toh bari na dauko miki lotion dinki ki shafa Saina dauko miki rigar sannu "

Shiru tayi dan ko Ido bata san su hada.

Shiya miko mata man ta fara shafawa sannan ya dako mata foguwar Riga marar nauyi.

Bayan ta gama shafawa ta sanya rigarta ta gyara gashinta sannan ta ja hijab dinta ta saka ta zauna ta tada sallah.

Yana ganin haka yayi maza ya nufi kitchen.
  Tea ya hada mata me kauri sannan ya soya mata kwai.

Bayan ta idar da sallah kwanciya tayi kan abin sallah tare da rufe idanunta tah.

Da sallama ya shigo dakin sannan ya zauna kusa da itah.

"Soulmate tashi kisa wani abun a cikin ki saikisha magani kinji"

Shiya taimaka mata ta zauna tare da cire mata hijab din,kwantar da ita yayi a kirjinsa tare da fara bata tea din.
   Babu musu ta fara sha sannan ya bata kwan.
  Saida ta ciye duka sannan ya rabu da itah.
  Ruwa ya dauko sannan ya ballo mata paracetamol ya bata tasha.

Sai shafa mata baya yake ahankali yana mata sannu.

Shiru nadan lokacin kafin yace "sannu kinji tawan kiyi hakuri baza'a kara bah kinji"

Daga masa kai tayi alamun ta hakura.

Tashi yayi tare da gyara gadon sannan ya kwantar da ita saman kirjinsa akan gadan suka koma bacci.



*★★*
Sai wajan *11am* ta farka amma har lokacin Fahad ya na bacci.

Ahankali ta mike tana dingisawa ta nufi toilet, kara gasa jikinta tayi ta kuma wanka sannan ta fito.

Nan ta shirya cikin Riga da wando ba Pakistan red.
Ta gaya gashin kanta ta feshe jikinta da turare masu kamshi nan ta koma kamar su.

Ahankali ta matsa kan gadan tare da tashin Fahad din.

Dama ya jima da farkawa yaganta tana shirya wa.

Murmushi yayi mata,da sauri ta fara kokarin tashi dan kunyarsa takeji.

Janyota yayi ta fada kan kirjinsa ta fada tana Murmushi.

"Soulmate har yanzu kunya ta kike ji uhmm!?"

Aa ta girgiza masa kai.

"Toh meyasa kike boyemin fuskar ki uhmm,bakyasan na rinka kallan fuskarne"

Shiru tayi ajikinsa,

"Toh tashi ki gayamin abunda kike so kinji Soulmate dina"

"Yaya nifa ba abunda nake so nagayamaka"

Juyar da ita yayi ya mata rumfa tare da fadin "har yanzu baki ji komai ba scdround za'ai.

Nan danan ta fara kwallah" Wallahi ban karawa daga yau Allah pls karka kasheni"

Dariya yayi tare da fadin "matsoraciya nima da wasa nake I Lov you matatah"

Rungumeshi tayi itama tare da fadin "Lov you more mijina☺"



*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Bayan Shaheeda ta dawo daga makaranta cikin zumudi ta shigo gidan dan bata da burin daya huce taga Mamantah duk dah bata santa bah.


Tana shiga tayi wanka ta shirya cikin Riga da skirt na atamfa tayi kyau sosai ta yafa Mayafin tah sannan ta fito.

Dakin Hajiya ta nufa dan ganin ta shirya.

Da sallama ta tura kofar tana zaune ta idar da sallah "aa Shaheeda barki dawo"

"Wallahi Hajiya dan karma na bata lokaci nayi saurin yin wanka dama nayi sallah a makarantah kawai kitaso mutafi"

"Tohhh kaji yarinya ko abinci bazaki Ciba sai kace zaki tashi sama"

"Wayyo Allah Hajiya ki taimaka Wallahi bazan Ciba ai cikina kawai ki taso"

"Toh Allah ya kyautah"
Ta fada tare da mikewa dan sutafin.


Dama driver n su na waje yana jiransu.

Suna fita sukai gidan Dr.Hussainah.


*★★*
Da sallama suka shiga tana zaune a falo da yake bata fita ran Friday.

Cikin fara'a ta amsa sallamar tare da basu wajan zama.

Bayan sun gaisa take tambayar yame jiki.

"Hajiya jiki Alhmdullh saide karin neman saukin Allah dan dazuma aka gama mata gaba daya addu'ar sai kuma batun tafiyama"

"Ohh! Allah mun godema,Allah ubangiji ya biyaki Hussainah ya azurta miki iyalinki ni Wallahi nama kasa cewa" Hajiya ta fada tare da fashewa  da kuka.

"Kai kai! Haba Hajiya dan Allah menene kuma abun kuka kede ai anzama daya saide a dage da addu'a kuma"

Shaheeda ma saida ta kara mata godiya,

Taji dadi sosai na ta kuma ganin kamar da suke da Maman tatah.

"Yanzuma zata fito taje tayi sallah ne da muna tare anan ai"

"Allah sarki ina kuwa Zainab Ku bata nan?"
Hajiya ta tambaya.

"Eh taje makaranta ansar wasu takardu amma maybe ki ganta nan ba da jimawa bah"

Ahankali take fitowa daga dakin harta shigo cikin Falon.

Da gudu Shaheeda ta mike tare da rungumeta tana kuka.

Murmushi Maryam keyi hade da kwallah,tare da kuma matse er tatah ajikintah.

Da er suka zauna Shaheeda takwa shige jikinta
Kowa sun bashi tausayi.

Nan suka gaisa Hajiya ta kuma yi matah ya jiki.

Dr.ce ta mike ta shiga dakin tah da alama zatayi wani abunne.

"Hajiya ina Sapna ta,ina yarinyata er aljannah?" Maryam ke tambaya idanta cike da kwallah.

Gaba daya wani saban kukan suka sake, "Maryam Sapna nanan zata dawo gareki insha Allah ki kwantar da hankalinki.

Shiru sai akayi ,Shaheeda kuwa banga Uwa kamar ta shige cikin tah.

Nan kuma ta fara tambayar mutane dan yaushe gamu.

Sun jima kafin suce zasu tafi.

Dr.ce tace da Hajiya ai zasu iya tafiya da ita babu matsala tunda jiki ya warware.

Sosai Hajiya taji dadi nan suka shirya har motah ta raksu.

"Amma banjo dadi bah dazan tafi ba muyi sallama da Zainab bah,amma dan Allah inkinsamu tym akawo mana itah"

Murmushi tayi Dr.tare da fadin "Insha Allah Nagode"

"Wallahi mune da godiya Allah ya biya ki"

Sannan suka nufi gida Shaheeda sai murna take famanyi.



*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Yinin Ranar babu inda Fahad yaje ko kofar gida dan bayasan barinta ita kadai.
  Ita kuwa sai faman zubamai shagwaba take yana kara rudewa.

Bayan sallar magariba ya mike tare da fadin "Soulmate kinga yau gaba daya ban duba Salma bah gashi ko masallaci bakyasan naje saide nayi agida bara naje nadawo.


Murmushi tayi amma wani mugun kishi takeji cikin ran tah"Toh Hubby saura kuma ka dade"

"Haba ni nama isa yanzu zan dawo kinji Matah"

Kiss ya mata a baki sannan ya juya ya tafi hannun sa hade da nata ya saki.

Da baya taba tare da jingina jikin kujera.
  "Ajjiyar zuciya tayi tare da fadin Allah ka ragemun zazzafan kishin dana ke ji" harda kwallah cikin idanta.


*★★*
Koda ya karasa part din Salma a kulle ya gansa.
  Gashi dare ne ga mamaki taya zata fitah batare data gaya masaba yana cikin gidan.

Wayar shi ya zaro daga cikin aljihu tare da kiransa.

Tana dagawa yace da itah "Ina kika tafi da wannan tym din?"

"Naga tun safe ka matah dani shiyasa nima nafita amma inakan hanyar dawoaw"

Tsaki yaja tare kashe wayar sannan ya fita dan yaji ana kiran sallar ishsha.






😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer*😘
[24/3 23:31] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
                👑👑
                   🌳
       *MARAICHI*❣
              *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
     *(Zeenaseer😘)*



7⃣7⃣




*•••••••••••*Bayan dawo dawo daga sallah part din Salma ya shiga ganin motarta a wajen.

Yana shiga cikin dakin nata da sallama.

Tsaya take ta gama canza kaya kenan tana gyara kan gadan.

Ahankali ta karaso wajansa tana wani rangwada tare da fadawa jikinsa yana tsaye.

"Meyasa kike fita batare dakin sanar dani bah"

"Pls kayi hakuri gani nayi Amarya ta tsareka shiyasa nikuma na fita naga baka zo kaga lafiya taba"

"Amma basai ki karani bah ko baki da wayane"

"Pls sorry baby nayi laifi amma dan Allah kayi hakuri"

Yaji dadi sosai yanda yaga ta sauko har tana bashi hakuri.

"Is OK but a kiyaye gaba"

"Insha Allah" ta faman shafa masa kirji.

Janyeta yayi tare da fadin dan doramin tea.
Sannan ya juya ya fice daga dakin.

Baki ta tabe tare da yin dariya"duk abunda kake bukata zanma zaku gane Salma ba wasa bace wlh" sannan tabi bayansa ta shiga kitchen ta Dora masa.

Yana zaune a falo yana kallo harta gama ta hado ta kawo masa.

Zama tayi kusa dashi tare da fadin "ina Amaryar take aka Sani dafa tea.

Shiru yayi mata yana zuba wa sannan ya fara sha batare daya ce da ita komai bah.

Itama shiru tayi masa taci gaba da kallan.

Sai bayan ya gama sha sannan yace da ita " naki nake bukata Nagode "tare da mikewa ya manna mata kiss a chick dinta sannan yace " gudnyt"

Ya fice daga dakin.


*★★*
Sapna kuwa ganin ya jima be dawo ba ta koma daki tayi shirin kwanciyarta ta haye gado dan danan bacci ya dauke tah.

Shima koda ya kullo ko ina yaga tayi bacci gadan ya haye jawo tah jikinsa tare da yi mata addu'a sannan ya lumshe idanunsa.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*

*BAYAN WATA DAYA*

Kamal na zaune saman kujera yana faman shan giyar sa sabo da tension yayi masa yawa,gashi Leon na binshi bashi ba adadi.

Gashi tunda Bash ya tafi Dubai shada Safiya har kwanan yau be dawo bah.

Gasan Sapna dake shirin illatashi.

Daga kwalbar yayi yayi jifah da itah.nan danan kuwa ta tarwatse.

Kansa ya dafa dan gaba daya yayi masa nauyi.

Tabbas dolene yadau mataki akan Fahad dan ko zai rasa ransa saiya auri Sapnar sa saboda itace farin cikin tah.

👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
Jikin Mama ya warke sosai dan har kebbi taje da katsina Amma Umma bata san da hakan bah.
   Ta kuma kyau jikinta ya dawo saide kullum itama cikin rokwan Allah take ya bayyana mata Sapna tah,dan Hajiya ta gaya mata komai.

Haka Shaheeda kullum itama tana addu'a da sauran en gidan.



Ban garan Zee kuwa tasha zuwa gidan Hajiya amma basu taba haduwa da Shaheeda da bah kullum tanasan su hadu in har taje .

  Tana zuwa gidan Sapna mah,su sha hirar su amma ba sosai bah.


*★★*
Fahad kuwa gaba daya hankalinsa yana kan Sapna yanzu ko office yaje arana sai suyi waya yakai so 10 barinma in ba ita kede girki bah.
   Itama ta cire kunya tana nunawa mijinta so da kuma kulawa.

Salma kuwa suna nan suna hada makircinsu ita da Safiya dan kullum tana gaya mata tana hanya amma har yanzu shiru.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Yau girkin Salma ne dan haka Fahad ba'a dakin Sapna yake bah.

Bayan sun gama cin abinci bayan ishsha eh yace da Salma bari yaje yayima Sapna saida safe.

Banza tayi dashi dan kullum inya tafi saiya dade yake dawo wa.

Yana nufar part din nata ya shiga dakin amma bata nan.

Toilet ya nufa ya tura ahankali, ganin ta yayi tsukunne jikin sink tana dauraye bakinta.

Tana mikewa ta tafi zata fadi idanta na lumshewa,da sauri ya tallafota ta fada jikinsa.

Gaba daya rudewa yayi yana kiran sunan tah.
Daukarta yayi ya dorata kan gadon yana kallanta, ta rame tayi fari sosai.

Dama shiyaga kwana biyu duk ta canza amma inyayi magana sai tace lafiayrta qlau.

"Soulmate" ya kira sunan ta yana kallanta.
Amma ita har tayi bacci.

Gaba daya yaji wani irin tausayinta ya kamashi dan yanda ta koma.


Ya jima akanta yana kallanta yana tunanin ko asibiti zai kaitane.


Ita kuwa Sapna yinin ranar Amai ta rinkayi da bacci ko abinci baraci sai ruwan zafi da Lipton ko shiga bata so.


Gyara mata kwanciyar yayi tare da kara rufeta da blanket din yana kara kallan kyakkyawar fuskarta.

*★★*
Ganin wajan *30mins* be dawo ba,yasa Salma tashi tare da binsa.

Ko sallama babu ta shiga dakin tana kallamai kira.

Har dakin da suke ta banko tana masifa "tsabar an raina min hankali,ga er iska kullum akazo sallama sai an haura tym toh Wallahi yau nagaji"

Sapna dake bacci farkawa tayi ahankali tare da mikewa zaune.

Shikuwa Fahad tsabar takaici kasa magana yayi.

"Hubby katashi ka tafi mana girkin tane"

"Soulmate bazan iya tafiya bah,ba faki da lafiya wazai kulamin dake"

Murmushi tayi tare da saka hannun sa cikin nata"hubby Allah, Allah natare dani jst go gudnyt"tana kaiwa nan ta saki hannun nasa tare da juyawa baya,wani irin kukane ya kwance mata wanda bashi da kara sai hawaye,ita kanta batasan kina menene bah.

Salma na tsaye Kansu tana jijjiga hannunta saman kugu kamar ta kashe Sapna dan haushi da kishi.

Badan yaso ba ya mike jikinsa a sanyaye ya matsa daidai kanta yayi mata addu'a tare da manna mata peck.

Sannan ya fita batare daya mata magana bah.

Juyawa tayi tare da fadin "shegiya ni zaki nunawa bariki karamarki dake" sannan tayi tsaki ta fice daga dakin.

Saida ya kulle mata kofar sannan ya fitah zuwa part dinsu.

Tunda suka koma bai kula taba dakinsa ya shige ya kwanta itah kuma tana falo.

Can anjima ta shigo dakin tare da hayewa gan gadan ta wani manne ajikinsa.

Shikuwa hankalinsa baya kanta gaba daya.

Haka ta gaji da romancing dinsa taga yaki kulata ta hakura tayi bacci dan bazata bari ya koma wajan Sapna bah koda zata mutu.

*★★*
Can cikin dare ta tashi ta rinka uban amai gaba daya bata da karfi duk jikinta yayi weak,ko yin kurin aman babu ta kasa.
   Tana kwance a tsakiyar dakin nata takasa motsin kirki ga zuciyarta sai faman tashi take ciki na ciwo.

Babu abunda take sai kuka kasa kasa,abun tausayi.


*★★*
Gaba daya daran Fahad beyi bacci ba,yana jin kiran sallah yayi maza yayi alwala ya nufi masallaci, ana idar wa kuwa ya nufi part dinnata.
  Jikinsa har rawa yake ya bude ya shiga dakin nata.

Kwance ya ganta kamar matacciya akasa babu abunda take banda hawaye de bin kumatunta wani nabin wani.

Da sauri ya karasa wajan tare da dagota yana kiran sunan ta jikinta yayi zafi zadau.

A kifime ya saka mata hijab ya nufi mota da ita.

Cikin gidan ya koma ya dauko key din motar ya dawo suka fita.

Ita kuwa Salma duk abunda ake tana can tana ta faman baccin tah ko ajikintah.


Yana isa da ita emergency suka yi da ita.
Fahad har kwallah yake dan gani yake kamar Sapna zata mutu ta barshi.

Jikinsa har karkawa yake ya Ciro fone dinsa a aljihu dan kiran Mum.

*★★*
Bayan ta idar da sallah tana zaune wajan *6am* saman sallama taji wayarta na kara.
   Ganin Fahad ke kira tayi mamaki da sassafan nan Allah sa lafiya de.
   Da sallama ta daga.

Yana jin muryarta ya fashe dakuka.

Gaba daya hankalinta itama tashi yayi "Fahad lafiya, waye ya mutu gayamin" ta rude tana tambayar shi.

Da ker ya yiya daidaita kansa tare da fadin "Mum Sapna ce gata a asibiti kamar zata mutu wallahi"

"Haba Fahad sai kace ba jarumi bah ka zauna kana kuka haihufa zama tayi tunda ita mace ce amma dan bata da lafiya ka zauna kana kuka,me ke damuntah?" Ta tmbya.

"Nima ban sanibah,daga amai da yakeyi ne sai zazzabi"

Murmushi Mum tayi tare da fadin "toh Allah ya sauwake gamunan zuwa.
Sannan ta katse wayar tare da girgiza kai harda er dariya tah " Allah ya shiryeka Fahad" ta fada.


*★★*
Bayan an gama duk taimakon da zasu mata suka saka mata drip tana kwance ta samu bacci.

Dr.ne ya kira Fahad zuwa Office.

Dayake nan ne asibitin zuwansa duk sunsabah.
Bayan sun gaisa Dr. Ya kika masa hannu suka yi musabaha kafin yayi Murmushi, *Congratulations Mr.Fahad ur wyf have 3wks pregnancy*

"Watt"😳😀ya zaru Ido yana murna dan dadi kamar yayi me rufe idansa yayi tare da yima Allah godiya.

Sosai yayima Dr.godiya albishir daya mai,sannan ya tambayeshi ya jikin me cikin.

" eh tah jiki da sauki nan da wasu hours zama a sallameku ,amma wani hanzari ba gudu bah,tana da Wata iriyar mahaifa kamar bata da kwarine sosai inta fita aiki ko wani tsale ko daukar Abu me nauyi gsky za'a iya samun matsala.
  Shiyasa cikin ke bata wahala,amma zan Baku magunguna intanasa zata samu saukin ciwon insha Allah "

"Nagode Dr.kuma insha Allah za'a kiyaye insha Allah Nagode sosai Nagode sannan ya kuma mika masa hannu.

Sannan ya fito ya nufi dakin da take dan ganin Rabin ransa.❤






😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷







*Written by Zeenaseer*😘
[24/3 23:31] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳         ⚜      🌳🌳
🌳                              🌳
                👑👑
                   🌳
       *MARAICHI*❣
               *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
     *(Zeenaseer😘)*




7⃣8⃣




*••••••••••••*Yana tura kofar dakin kwance ya ganta saman gadan tana faman bacci.
   Kujera ya janyo kusa da ita ya zauna ya zuba mata Ido yana kallanta ji yake kamar ya maidata cikinsa dan sosaiya.
  Ahankali yasa hannu yana gyara mata gashin daya dan rufe mata fuskarta.
   Ahankali tadan motsa kadan da sauri ya janyo hannun nasa dan karya tasheta.

Gaba daya ji yake kamar anmai albishir da zai shiga aljanna"yau shi Fahad za'a haifama da ko yar,yau shine matarsa keda ciki,yau shine zai zama Baba"
   Ahankali yasa hannu yana share kwallar data fara zubowa.

"Sapna koda kina jina ko bakya jina ya zama dole na fada,kin gama min komai a rayuwata,kece duniyata,kece rayuwa tah,kece farin cikina,kece duk wani motsi nawa,Sapna bazan iya fada miki Wata iriyar mace kika zamo cikin rayuwa tah,tabbas Allah yayine ne danke Sapna badan kowa bah,Sapna baki caccanci na hada sanki dana kowa cikin zuciya tabah,duk wani gata dazan nuna miki Wallahi bazan taba iya biyanki farin cikin da kuma walwalar da kika Sani acikin rayuwa tah bah,na tabbata Allah ba karamar kyatah ya yimin bah amatsinki na mata tah bah,kece komai nawa Sapna Allah ubangiji yayi miki albarka sannan yasaki cikin jannatul firdousi,Allah ya baki duk abunda kike na duniya da lahira"

Ahankali ya kamo hannun ta ya hada da nasa ya manna mata kiss a hannun tare da fadin "dan Allah Sapna karki tafi ki barni ki zauna tare dani har karshan rayuwtah kece komai nawa Sapna Nagode matata wanda ta kasance abun alfaharina Nagode Sapna Nagode Allah ya biya ki"

Harda hawaye sa saboda yana jin Sapna acikin ransa,duk wani bugun zuciyarsa dayake da kuma motsinsa da numfashinsa yana jinsune tamkar sapnarsa.
   Baya fata randa zaiga rabuwarsa da ita.
   Rungume ta yayi yana ci gaba da kwallah.
   Tabbas Sapna ta ciri tutah,ta maida jarumin namiji tamkar karamin yaro sabo da soyayyar tah.
  Gaba daya Fahad ya zauce sabo da so da kuma kaunar da yakema Sapna.



Ahankali ta sanya hannayanta tare da kuma matsesa ajikin ta tana kukan itama.
   Da sauri ya mike tare da fadin "Soulmate kin tashi sannu ya jikn naji kina bukatar wani abunne uhmm!"

Kara fashewa tayi da kuka tare da rungumeshi "nima ina sanka bana fatan Allah ya rabamu har karshan rayuwarmu,burina koda yaushe najini tare dakai Hubbyna" I Lov you a rwwly Lov you my one nd only.
Suna rungume da juna aka fara kwankwasa kofar.

Da sauri ta janye jikinta daga danashi sannan ta goge fuskarta shima haka.

"Yes come in" ya fada yana kallan kofar.

Mum ce ta shigo da sallama rike da kwando a hannunta na abinci.

Sapna na ganin ta tayi saurin mikewa zaune tare da sakin Murmushi.

Amsa mata sallamar sukayi sannan ya amshi abincin hannu nata ya bata waje ta zauna.


"Gaisawa sukayi da fahad sannan ya koma gefan Sapna ya zauna Damma ita kunyar Mum din takeji.

" inkwna mum"ta fada tare da sunkuyar da kanta.

"Lafiya qlau Sapna ya jikin naki Allah ubangiji ya saukeki lafiya"

Durkusar da kanta tayi matare data kuma kallan Mum din bah.

Fahad shikenan kuma tunda akayi aure aka Saina xuwar mana sai anga dama"

Sosa kai ya fara tare da fadin,Wallahi mum aikin office yayi yawa ga kuma gajiya shiyasa amma ina san na shigo itama tana san ta rinka zuwa ai" ya fada yana kallan Sapna.

"Toh Allah ya bada sa'a ya taimaka"

"Ameen ya fada"

Sannan ta kuma kallan Fahad din tare da fadin me likitocin sukace " Nan yayi mata bayanin komai batare daya boye mata bah"

"Toh Allah ya raba lafiya ya kuma bada zuri'a na gari,kaga saika hadu mata kayanta ta dawo gida tunda kaga halin da take,da ace kan gidan naka ahade yake sai a barta amma kaga yanzu babu me taimaka matah,ko kuwa"

Nan danan yaji kamar an caka masa mashi a zuciya.
"Haba Mum insha Allah zata samu kulawa ta musamman anan din mah"

"Uhmm kasan Allah Fahad bazata koma gidan nan bah,so kake mutu,kalli yanda ta koma yanzu haka bama tacin abinci,duk ta rame ga ciki.
Yaushe mah hakan zai yiyu,inkasa kafa ka fita bame dubata harsai ka dawo da yamma"

Shiru yayi dan ba yanda ya iya amma bazai iya rabuwa da matar shiba.

Itama tunda suka fara bata saka musu baki bah dan ita so take tabi Mum kota samu Hutu ko danshi Fahad dayake mabukaci,ga aikin gida ga bata da lafiya.


*★★*
Karfe *2:pm*aka sallamesu sannan fahad ya kaisu can gidan Mum din.

Amma ba'a san ranshibah.

Haka ta shiga da ita tayi wanka taci abinci ta koshi sannan ta kwanta dan hutawa.

Shikuwa Dad ya kira a waya ya shaida masa shide yayima Mum magana gaskiya abashi matarsa.

Nan Dad yayi ta dariya yace inya dawo da yamma yaje ya dauketa.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Lokacin da Salma ta bataga  Fahad bah tayi tunanin yana wajan Sapna nana bala'inta ya motsa ta tashi ko sallah batayiba ta nufi part din Sapna amma ta bincika basanan sai da ta lura daya fita da mota sannan tayi tunani ko sun fitah,toh amma ina Fahad zasu da sassafe lau.
   Koda ta kirashi awaya be daga bah,hakan yasa ta kuma kuluwa,in banda yana raina mata hankali ranar girkin nata zai dauki kishiryata ya fita da ita bama tare da sanin taba.Wallahi bazata yarda bah sai tadau mataki.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Bayan ishsha Fahad ko kunya Babu yaje daukar matah,da ker Mum ta yarda tare da sharadin taji fim! er matsala zata daukotah koda kuwa me zaiyi.
   Haka kuwa ya amince badan san rantabah ta barta tanata faman hararar shi.

Haka ya dauko matarsa suka shiga motah sai Gidah.

Suna tafiya cikin motar ya juyo ya kalle tah,
Idanta alumshe tana jin karatun kur'anin daya kunnah.

"Soulmate" ya kira tah

Batare data bude idan bah ta ce "uhmm!"

"Bakyasan ki biyoni koh?"

Gyara zamantah tayi,tare da fadin "amma meyasa bazaka barni wajan Mum bah ina ganin zamufi samun kulawa nida bbymu kokuwa"

"Uhmm hakane amma nafi bukatar hakan akan Mum cos always am in need wit U"
Ya fada tare da shan kwana.

Shiru tayi kafin tace "but Wallahi bazanji dadi bah saboda infah ka tafi office sai yamma gashi bani da cikakkeyar lafiya"

"Hakane ki zauna zan sama mana yarinyar da zata na taimaka miki right"

"Shikenan dai Allah ya karamin lafiya"

"Ameen" ya fada tare da tsayawa kofar gidan yana horn.

Bayan me gadi ya bude yayi parking ya bude matah ta fito.

Saida ya kaita daki ya dauko mata duk abunda take nemah sannan yayi mata sallah tare da ce matah "da taji ciwo ta kirashi a waya" sannan ya fitah.


*★★*
Lokacin daya shigo part din Salma tana daki a kwance.

Yana shigowa ya rungumeta yana farin ciki.

Kallan shi kawai take da mamaki.

Murmushi ta danyi tare da fadin "lafiya kuwa na ganka haka"

"Bby dole mana nayi murna kema na gaya miki saikin tayani murna"

"Toh gayamin mana inji"

"Albishirinki"

"Goro" ta fada tana kallansa.

"Mun kusa samun kidz a gidan nan"

Dammmmm! Zuciyarta ta buga.

"Me kace" ta kuma tambayar sa tare da mikewa zaune.

Ta baya ya rungumota yana Murmushin "I mean Sapna Nada ciki"

Wani kululun bakin cikine ya tsaya mata cikin zuciyarta wanda ya haddasa kafewar miyan bakinta gaba daya.

Murmushin dole ta kwakulo tare da juyowa ta fuskance shi "wow gaskiya muna farin ciki yajikin natah?" Ta tmbya.

Shikuwa baki har kunne yafada "da sauki "
Sannan ta rungumeshi dan Wata iriyar gobarar bakin ciki kecin zuciyarta kamar tayi me.

Shima rungumeta tan yayi.


Har yayi bacci amma Salma ta kasa bacci zaman dakinma kasawa tayi ta koma falo tanata faman safa da marwa. Ta rasa abunda ke matah ddi.






😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer😘*
[24/3 23:31] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                  🌳
     *MARAICHI*❣
               *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
     *(Zeenaseer😘)*




7⃣9⃣


*Dedication to you my dia Bellzahra❤😘*




⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
*•••••••••••*Bayan Fahad ya dawo daga sallah part din Sapna ya koma.
   Zaune ya ganta kan sallaya ta idar da sallah.

Bayan ta gaida shi ta maida abin sallah sannan ta fito daga dakin.

Tasowa yayi tare da biyotah,kitchen yaga ta nufah.

"Soulmate me kuma zakiyine da sasaafe a kitchen pls banasan kina wahalar da kanki fah pls"

Juyowa tayi fuskarta dauke da Murmushi ta shafa gefan fuskarsa tare da fadin "Hubby bbynmu najin yinwa shiyasa zan samu nasa wani Abu abakina"

Rike wannan yayi tare da janta ya zaunar da ita saman sofa.

"Zauna bari na hada miki me kike so"

"Tea kawai bake so amma banda madara Milo kawai zaka sakamin"

"Angama kinji bari naje na kawo"

Kitchen fin ya nufa ta bishi da kallo tana Murmushi harya shige.



Bayan few minutes ya shigo falon da cup din tea din ya mika mata.

Harkan kujerar ya zauna tare da janyota jikinsa ya saka mata cup din abaki ta fara sha.

Ahankali ya dinga bata harta shanye gaba daya.

Sannan ya maida cup din ya zauna yana kallanta.

"Hubby meyasa baka gajiya da kallo nane" ta da hura mai iska a idansa.

"Soulmate bana gajiya da kallanki nima basan meyasaba" yana magana tare da Dora hannunsa saman Marartah yana shafawa.

"Soulmate me kikesan Allah ya bamu inkin tashi haihuwa?"

Murmushi tayi me sauti "duk abunda Allah ya bamu muna bukata me albarka amma inasa twins"

Kiss ya manna matah a kanta sannan ya kara kankameta ajikinsa "Ameen matatah"

Da sauri ta janye jikinta tare da shagwabe fuska "Haba Hubby bafa girkin bane sai anjima zan amsa kuma ka taho kabar Aunty karfa ta rama kasan bazanji ddi bah"

"Ai itama tasan baki da lafiya na gaya mata"

Shiru tayi tana kallan sa "amma de kaga babu ddi ka koma abunda kwana biyu muna tare pls kaji"

"Toh" ya fada tare da mikewa ya kara mata peck a goshi,ahankali ta rufe idanta tare da riko hannunsa sa tayi dage itama tayi masa sannan ta nufi daki dan itama tana jin yanda yakeji ga kishi"

Binta yayi da kallo sannan ya juya ya fice daga part din.


*★★*
Gaba daya tunda Salma taji batun cikin Sapna ta rasa sukuni,banda bakin ciki babu abunda ke cinta gaba daya ta tsani kanta da rayuwar tah.

Duk tabi ta shiga damuwa,duk mun bakin cikin data sha lokacin auran Sapna bekai wanda take fuskanta a yanzu bah.

Tabbas tana cikin tashin hankali da bala'i mundun ta bari Sapna ta fara tara yara cikin gidan nan.



*AKWANA ATASHI BA HUYA WAJAN ALLAH*
   Yau cikin Sapna yakai Wata hudu dan harya fito,tayi kiba tayi kyau dan tana saman kulawa wajan Mum da kuma Fahad.

Kullum zata ci ta kwanta ta kara haske tayi kyau da itah.

Zee mah na zuwa tana ganin ta amma har lokacin basu hadu da
Mamah da Sapna bah suma kullum fatansu kenan suga Sapna.


Salma kuwa damuwa kamar zata mutu duk lokacin da taga Sapna da uban ciki.

Safiya mah ta dawo amma har lokacin bata shigo gidan nasubah.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Tana zaune saman kujera da cikinta tana ta faman shan mango ga wayarta a kusa da itah.

Kiran Zee ne ya shigo cikin wayar tata.

Dauka tayi tare da karawa a kunnan tah.

"Me ciki" Zee ta fada tana dariya.

"Zee bana san iskanci tam,yakk ya gidan dasu mamah"

"Wallahi kowa qlau ya karfin jikin naki"

"Jikifah Alhmdullh na warware yaushe zakizo"

"Hhhh baki da aiki sai tambayata yaushe zanzo,dama yau zanzo na ganki"

"Ywwa kawata dama kuwa saura ni kadai ce pls ki tawomin da abun kwadayi kinji"

"Insha Allah Saina zo"

Sannan sukayi sallama tana ta murna Zee zata zo.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Zaune Safiya da kuma wasu mata su biyu saman kujera kana ganin su kaga gogangun in duniya sai Salma agefe daya kana ganin tah tana cikin damuwa.

Safiya ce ta kalle tah tare da fadin "Salma Wallahi kina bani mamaki,yanzu duk iskanci da kishinki ace wannan yarinyarce ta tsone miki Ido"

Wallahi kika bari ta fara haihuwa gidan nan kin shiga uku,Wallahi banza mah ta ciki "


"Safiya kenan ba haka bane ya kikesa nayi yanzu niba abinci mukeci da itah bah ba wani Abu bah amma kai ni nama kasa cewa komai"

Zamanta ta gyara tare da "Fadin kinga kalleni dakyau ki gani,kinga wa dan nan " tana magana tana nuna matan nan guda biyu.

"Sabo dake na dauko su basu da imani ko kadan yanzun nan inkina so sai a gama da ita da cikin gaba daya"

Da sauri ta dago tare da kallan Safiya "Amma kinsan ni  za'a zarga tunda ba kowa cikin gidan saini da itah"

"Banza ai komai da hankali ake yinsa,dakata yanzu suna gama aikinsu zamu fita tare koda anzo bama kyau gidan"

Kwashe wa tayi da dariya "gaskiya kawata kin rika Nagode sosai bara na dauko veil dina kawai suje toh"

"Ywwa koke fah" ta juya ta kalle su tare da fadin kunga ai part din dana nuna muku ko?"

Gyada Kansu suka yi alamun sun gane.

"Ywwa basaina muku bayanibah kuyi maza zamu fitah.

Sannan suka mike.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Ita kuwa Zee tanaso suyi magana da Sapna dan ta gama gano Sapna er Maryam ce tana san bata surprise shiya taje can gidan ta roki mamah data bata Shaheeda zata rakatah wani waje amma bata sanar da kowa bah.
   Shaheeda taci kwalliya dukkansu tana san basu surprise ne shiyasa tayi hakan.
   Hajiya kuwa ta sanya driver ya kaisu.


Suna cikin tafiya Shaheeda ta kalli Zee tare da fadin " Ya Zainab dama wallahi inasan nadan rinka fitah Saina rinka ganin kamar zanga ya Sapna.

"Hhhhhh kai Shaheeda yanzu in kikaga Sapna zaki iya ganetah kuwa"

Hmmm "mezai hana ko rufe idona nayi ina fanin kamanin tah,Allah sarki yayatah munsha gwagwamar mayar *MARAICHI* a rayuwa Allah ya saka matah da alkhari yasa tana hannu na gari inkuma ta mutu Allah ya kaita aljanna" tana maganar tana kukah.

Itama Zee saida tayi kwallah.

Ahankali ta Dora ta kan kafadarta tare da lallaahinta "insha Allah kin kusa Saina *MARAICHI*ntah zata dawo gareku cikin farin ciki.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
 Fahad ne ke ta faman kiranta da sauri ta daga tare da karawa a kunne.

" Pls Hubby am srry ina toilet ne,ya office din"

"Ajjiyar zuciya ya ajje tare da fadin Alhmdullh"

Murmushi tayimai "lafiya mijinah"

"Soulmate Wallahi tun dazu gabana ke faduwa kina lafiya kuwa gani nake kamar wani abun ya faru dake"

"Hmmm! Mijina lafiya qlau nake bbynmu ma lafiyarshi qlau kina bashi wayar " ta fada tana dariya"

Wani mugun tausayintane ya kamashi harda kwallah shine har yanzu hankalinsa be kwantah bah"

"Soulmate bazan iya zaman office din bah inasan nazo naganki"

"Hubby qlau fah nake pls karkabar aikinka I Lov you kaji kaita addu'a zakaji ddi a ranka"

Idansa ya rumtse tare da fadin I Lov u too"

"Ywwa nawan nayi baki naji sallama bari naje inna dawo zan kiraka"

"Ohk I Lov matatah I Lov you take care"

Itama wani irin taji sannan ta katse wayar ta fita falon.


Zaune tagansu kan kujera su biyu.

Da Murmushi ta karaso wajansu tare da fadin "sannunku da zuwa" duk da bata gane su bah.

"Ywwa sannu sukace"

"Ina yininku " ta gaida su.

Bayan sun amsane ta nufi kitchen dan dauko musu abunsha.


*★★*
Fahad koda suka gama wayar shide jikinsa na basa da matsala da sauri ya dauko key dinsa ya fito dan dawowa Gidah.

*★★*
Dauke da tray da juice da ruwa samansa da kuma kanana kofuna,
Ahankali ta karaso dan ajjewa gabansu.

Tana durkusa daya daga cikin matan ta  caka mata huka acikin tah.

Da sauri ta dago tana kallan tah tare da dafe cikin nata ta saki tray din idanta harya yi jah.

Zare hukar tayi itah kuma Sapna tayi baya ta bugu da kujera ta fadi kasa ta fara jah da baya a kwancan hannun tah dafe a cikintah tana dago dayan hannun sama alamun su rabu da itah.

Jini duk ya bata tiles din dakin .

"Dan Allah karki kasheni,kutausayamin ciki fah gareni kodan jaririn dake jikina " tana magana tana kuka.

Dayarce ta rugo tare da taka mata cikin da karfi.

Wani irin ihu ta saki da karfi.

Tsaye suka tayar da ita nan danan jini ya fara zubowa ta kasanta.

Duka suka shiga yimatah duk suka fasa mata,baki,hanci,kai amma duk da haka basu kyaletabah ganin har lokacin tana numfashi.

Hukar suka kara caka mata sannan suka yarda itah suka fice daga gidan.

Tana kwance a kasa cikin jini sai hawaye kebin gefe da gefan idanta kamar tana raye kamar ta mutu.



Fahad kamar zai tashi sama dan tsabar gudun da yakeyi
Zuciyarsa sai faman bugawa take da karfi.

Suna komawa dama cikin motah suka iske su Salma nan  suka bar gidan.

Suna fita ba jimawa motar su Zee ta shigo.😞😞






😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷





*Written by Zeenaseer😘*
[24/3 23:31] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳         ⚜      🌳🌳
🌳                              🌳
                👑👑
                   🌳
     *MARAICHI*❣
            *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
    *(Zeenaseer😘)*



8⃣0⃣




*HBD Sis Mhizdijah wish u long lyf nd prosperity Babeehh!*🎂🍦🍭🍾😍😘❣



⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
*•••••••••*Motarsu na shigowa cikin gidan tayi parking daidai parking space sannan suka bude suka fito.

"Karka tafi bazamu jima bah yanzu zamu fito*Zee tace da drivan sannan suka nufi part din.

" Shaheeda! "Zee ta kira sunan tah

" Naam" ta fada bata tare data kalle ta bah

"Kinsan nan inane?" Ta tambayetah.

"Kai kema de ya nida ban taba zuwa bah taya zan san ko ina ne amma gaskiya gidan yayi kyau"

"Toh na gidan Sapna ne Shaheeda"

Cak ta tsaya tare da kallanta cike da mamaki a fuskarta.

"Taya kika san Sapna ya Zainab"

Batare data mata magana bah ta kama hannu ta suka shiga cikin gidan da sallama.

Ita kuwa Shaheeda tama kasa magana kawai bin Zee take taga ikon Allah.

Shiru ba'a amsa musu sallama bah gashi kuma falon duk a hargitse.

Gaba daya jikinsu yayi sanyi jin shiru gidan ga basuga kowa bah.
  Ahankali suke kara shigowa cikin falon har suka zo karshan sa.

Da gudu suka nufi gurin da suka hango Sapna a kwance cikin jini.

Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un kawai Zee ke furtawa.

Shaheeda kuwa mutuwar tsaye tayi ganin gata ga ya Sapna amma kamar amace dan ko motsi batayi.

Wani irin ihu ta kwallah tare da nufar tah da gudu.

Jijjigata ta shiga yi tana kuka.

"Wayyo dan Allah ya Sapna ki tashi ki ganni gamu munzo gare ki mama ma nacan tana jiran ki" kuka sosai Shaheeda take me tsuma rai haka itama Zee kwallah kawai take sharewa.

Da ker ta iya furta "Shaheeda taimaka mu fita da ita akaita asibiti dan Allah " itama kukanne ya kwace mata gainin irin mugun halin da Sapna ke ci.

Suna kokarin daukarta Fahad ya shigo falon da gudu yana kiran sunan tah.

Ganin ta a kwance ga su Zee gabanta duk jini ya bata musu kaya yasa shi kara sowa yana kiran sunan tah.

Kamar za rarre haka ya koma sukuwa basu da aikin daya huce kuka.

"Sapna! Sapna!! Sapna!!! Tashi gani nazo dan Allah ki bude idanki ki ganni nine Fahad dinki ki taimaka min dan Allah karki tafi ki barni Sapna waya miki wannan aiki dan Allah ki tashi" tuni shima ya fara hawayan.

Ko takan su Zee da suke zaune suna kuka be bibah ya dauke ta sai cikin mota suka nufi asibiti.

Da gudu suka fito suma daga gidan dan binsu a baya.

Shaheeda ta yarda dankwali,mayafi da takalmi ahaka ta karaso wajan motar a zare tana faman kuka.

Cikin motar su suka shiga tare da fadama driver yayi maza yafi Fahad daya jah motar kamar zai tashi sama.

 Nanvdanan shima ya bisu da gudu.

Lokacin dasu zee suka isa har an tafi da Sapna babu kowa a wajan sai Fahad zaine kan kujera yayi tagumi sai gumi yake hadawa ya cire tie dinsa ya ajje a gefe idansa sun kada sunyi jajir fuskarsa da hancinsama sunyi jah.
Kana ganin shi kaga wanda yasha kuka ya koshi.

Jiki a sanyaye suka nemi waje suka zauna.

Zee ce tayi karfin hali tana kuka ta dauko wayarta.
    Maryam ta kira bata jima tana ringing ba ta dauka tare da sallama.

Fashewa Zee tayi da kuka dan tama rasa me zata fada matah.

Hankalinta ne ya tashi "lafiya Zainab kike kuka ko accident kuka ne"

Kamar tana kallanta ta kasa magana kawai girgiza mata kai takeyi kamar tana kallan tah.

"Kiyi magana mana Zainab Wallahi hankalina ya tashi sosai ki gaya man"

"Aunty muna General hosptl kizo" shine abunda ta iya fada kenan ta yarda wayar tare da fashewa da wani saban kukan dan tayi mugun shiga rudani tabbas tasan Sapna mutuwa zatayi shikenan an rabasu.


Gaba daya hankalin Maryam ya tashi dan tun fitarsu takejin faduwar gaba shedai hadari zasuyi.

Mazatayi ta fama Hajiya itama hankalinta ne ya tashi dan harta fara kuka.

Haka suka fito suka nufi asibitin dan sun rude.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Motarsu na fita daga gidan suka sanar wa dasu Salma sun kammala komai nan suka hau dariya sannan Safiya ta biyasu kudin su suka sauka sukayi tafiyarsu.

"Gaskiya kawata Nagode dan kin mugun Sani farinciki yau"

"Hmmm kede bari ninamaso naga yarinyar ko ya take"

"Hhhhhh! Shegiya ki mata me kuma aina gaya miki er tsintuwace aka aura mai amm kinji sunan ta am! Yawwa Sapna! Sapna!! Ne sunan tah"

Da sauri ta juyo ta kalleta tare da fadin "Sapna kuma?"

"Tabbas haka nace lafiya naga kin shiga damuwa"

"Kikace er tsuntuwa ce"

"Eh"

"Ya kamannintah suke?"

"Uhmm ba Wata babban bace tana da karamin jiki,kunya ,kuma kyakkyawace ba laifi"

Gaba daya jikinta yayi sanyi "am...h.Salma anya ba kanwata bace kuwa"

"Kanwarki kuma gaskiya da er dan banga alama bah,ke muje dallah bama itah bace"

Hakanan taba amma hankalinta nacan tana tunani yanda zata ga matar ko Sapnar suke.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Jikinsu na rawa suka shigo cikin reception din dan tambayar ko zasu gansu.

Suna zaune sai Fahad deke nesa dasu wanda kana ganin sa ya fita daga ainun hankalinsa.

Shaheeda na ganin Mama ta rugo tare da rungumeta tana kuka sannan sukaga Zee a zaune.

Kallan juna sukayi kafin su karasa wajan su Zee din.

Shaheeda kamar zararriya ta koma.

"Zainab lafiya wai meke faruwane yanaga jikinku duk jini Ku mana bayani"

Ahankali ta dago jajayan idanunta tare da nuna Fahad da yatsarta.

Gaba dayan suka kama kallan shi da mamaki
"Lafiya waye wacan din"

Cikin rawar murya Zee tace "Shine mijin Sapna"

Gaba daya suka zaro Ido suna kallansa sannan suka kalli juna "Sapna fah kikace Zainab kinsan Sapna dama?"

"Aunty tare mukayi makarantah da itah har tayi aure nan ta fada musu abunda ta Sani game da Sapna"

Gaba daya sallati suka fara yi.

Lokacin Dr.ya karaso tare da fadin "kaine kuka kawo patient"

Da sauri fahad ya mike tare da fadin "eh ehh!! Nine"

Glass din idansa ya zare tare da dafa kafadarsa.

Suma gaba daya sun nutsu shi suke saurarah.

"Matarka tana cikin mahuyacin hali wanda mu kammu bamusan awani matsayi take bah na rayuwa ko mutuwa sanadiyar sukar huka biyu da aka matah da kuma cikinta da aka buga,
  Gaskiya saide kayi hakuri dan munyi iya kokarinmu mu taimaka amma hakan ya gagara amma bamusan ya ta Allah zata kasance bah yanzu muna bukatar jini akuma gwadaw"


Tuni Shaheeda ta yanke jiki ta fadi dan atunanintah ta mutu.

Fahad kuwa hawaye kawai ki zubah yana rasa taya zaiyi magana dan wani Abu daya tsaya masa a makogarunsa.

Kowa ya kado dan Hajiya kafafunta sanyi sukayi ,Zee mah batajima me Dr. Ke fadi bah haka Maryam kuka take.







😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer😘*
[24/3 23:31] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
                👑👑
                  🌳
     *MARAICHI*❣
              *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
      *(Zeenaseer😘)*



8⃣1⃣





*•••••••••*Da sauri suka nemi ruwa suka zubama Shaheeda ta farfado.
    Bayan nan Fahad ya kalli Dr. Tare da fadin "Dr.mezai hana dan Allah muje a auna jinin nawa inyayi basai a saka mata bah ataimaka" ya karashe maganar kamar zaiyi kuka.

"Babu kamai muje din"

Tafiya sukayi dan a dauki jinin nasa a saka mata ko Allah zai sa adace.



Mamah ce tadaga hannu sama tare da rokaon Allah ya bama yrta lafiya.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Har lokacin Salma da Safiya suna tare suna gidan Safiya.

Zaune suke cikin falon Safiya, gaba daya kana kallan Safiya zakasan tana cikin damuwa dan gaba daya hankalinta yayi mugun tashi dan gani take kamar Sapnar su ta sa aka kashe.

"Haba Safiya" Salma ta fada.
"Yazaki damu kanki,ai in akwai wanda ya kamata ya damu nice domin kishiya tace kuma mu biyu ke zaune cikin gidan kinga kuwa ai ni za'a tun kara"

"Salma kenan hakane amma hankalina be gama kwanciya bah,dama na gaya miki na taba ganin tah anan garin wlh"

"Haba dan Allah kibar damuwa bama itah bace,ni yanzuma bansan yama zanyi bah dan wlh bana san komawa gidan"

Safiya ce ta kalle ta tare da fadin" kinga ki kira Fahad ki dan nuna kamar bama kisan abunda ke faruwa bah bama kya gidan"

"Hakane fah kin kawo shawara" ta fada tare da dauko wayarta ta yi dailing numb.sa amma gabanta nadan faduwa"
    Harta gama ringing ta katse amma be daga bah,kallan Safiya ta kuma yi sannan alamun yaki dauka.

"Ki kara kara gwadawa mana" ta fada ahankali.
   Amma kusan sau 10ta kira amma yaki dauka.
  Hakan ya sanya hankalinta ya kuma tashi.

"Bari zuwa anjima maybe yana wani abunne"

"Toh " ta fada "Allah yasa besan abunda ke faruwa bah.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Sai wajan magrib sannan Fahad ya fito dan har an junama Sapna jinin.

Wajan su Zainab yazo ya zauna.

" sannu kaji Allah yayi maka albarka ya bama matarka lafiya kaji"Hajiya ta fada.

"Ameen" su mama suka amsa.

Zainab ce ta cema fahad "Fahad wannan fa Maman Sapna ce wannan kuma kanwarta sai kuma kakarta"ta fada tana nuna su.

Binsu yayi da kallo yana mamaki dan kan shima ya daure.

Zee ce ta shiga yimai bayani dallah dallah yanda zai gane.
  Nan yayi murna sosai sannan ya kara gaida su.
  Sosai sunji dadi nan suka tayi masa addu'a suna saka masa albarka.

Wayar shi ya dauko tare da fadin " Bari na kira Mum dan nasanar da ita.

Yana kira ta dauka tare da fadin "Fahad lafiya kuwa inata kiran Sapna bata dagaba kamai hakan"

Rasa ma me zai ce mata yayi sannan yace "Mum muna general hsptl kizo" abunda ya iya fada kenan sannan ya kashe.

Mikewa yayi tare da fadin bara naje nayi sallah sannan ya fita.

Suma tashi sukayi dan suyi sallah.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Bayan sun idar da sallah suna zaune Zee ta hango Mum tana shigowa itama duk hankalinta ya tashi.

Ganin Zee yasa ta nufi wajansu da sallama sannan ta zauna.

Gaisawa sukayi dasu sannan ta kalli Zee tare da fadin "lafiya Zainab meya faru ina Fahad din"

Nan Zee ta shiga hawaye tare da sanar mata abunda ya faru sannan ta gabatar mata da su Shaheeda.

Mum kuka ta shiga yi dan tana mugun tausayin Sapna kuma duk laifin fahad take gani dan tace dashi "yabar Sapna inta haihu ta koma gida" amma yaki yarda.

Cikin kuka ta fara fadin "Saida nace da yaran nan karya tafi da er nan amma yaki yarda duk da nasan tsautsayine.

Lokacin ne Fahad ya karaso wajan ganin Mum na kuka shima hankalinsa ya kuma tashi.

" da ker ya iya fadin sannu Mummy "

Ko kallansa batayi bah "Fahad ka kyauta,Wallahi Sapna ta mutu saide ka nemi Wata uwar bah niba,dama ai ba santa kake bah burinka ya cika ka maidata gidan gashi nan babu tausayi zasu kashe man itah"

Kuka yakeyi dan abunma ya kasa cewa komai.

Hajiya ce ta budi baki tare da fadin"be kamata ki yanke wannan hukunci bah,yaro nasan matarsa sabo da Allah dame kikeso yaji da fadanki koda ciwan matarsa"

"Hajiya Wallahi yaran nan kiri kiri nayi dashi yabaraman ita dan cikin na wahalar da ita amma yaki yarda"

Mama ce tace "tsautsayine ayimasa hakuri yana kaunar matarsa"

"Bari likitan yazo canza mana asibiti za'ai naga kafarka acan"

Shide kanshi na kasa idansa yayi jajir dan bashi da bakin magana zuciyarsa sa kuna take.

"Aa kiyi hakuri abarta anan din dan Allah" mama ta kuma rokontah.

"Nayarda amma ya tashi yaban guri"

Haka ya mike jiki a sanyaye dan ba yanda ya iya yabar wajan gaba daya ya ma rasa abunda ke masa dadi.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Har *12am*  suna nan zaune dan dan jiran saka makon Likita haka shima Fahad yana ta faman jira.

Dr.ya shigo wajan nasu tare da samunsu zaune.

Shikuwa Fahad na gefe dan yasan halin Mum.

"Toh Alhmdullh saimu godema Allah ta far fado Masha Allah"

Gaba dayansu Murmushi suka kama harda masu kukan dadi.

Mum ce tace da likitan "toh Dr.ya cikin nata yana nan qlau ko kuwa babu shi?"

"Eh toh duk da cewar Anyi matah suka biyu na huka duk basu taba cikin bah saide dukan da aka masa tade zubar da jini da yawa amma cikin be zube bah saide yana bukatar kulawa ta musamma"
  Fahad rungume Dr.yayi dan murna yana hawaye tare da masa godiya.

Cikin zumufi Shaheeda ta ce "Dr.zamu iya ganin ta yanzu?"

Murmushi yayi sannan yace "tana hutune yanzu saide zuwa Safiya maybe lokacin ta farka"

Allah ya kaimu duk suka fada.

Dr.ya kara fadin sai "mutun daya ya zauna sabo da tsaro"


Mum ce tace ita zata zauna,haka suka hakura badan sunsobah suka tafi.
  Dan Zee mah ta sanar da Maman tah saide ta kwana wajan su Shaheeda.

Har wajan mota Mum ta rakaso sannan ta dawo ciki.

Har lokacin Fahad na zaune.
Ko ta kanshi bata biba ta huce inda zata kwantah.


Shide yasan bazai iya tafiya gida bah dan yaso kwana anan.

Tashi yayi ya shiga motah sannan ya nufi gidan.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Salma tana dakinta a kwance tana ta tunani har lokacin bataji karan shigowar motarshiba.


Tana zaune taji shigowar sa.
Da sauri ta mike ta nufi window dan ganinsa.

Koda ya fito daga mota hasken fitilar ya haske fuskarsa gani tayi duk yayi wani iri.

Gabantane yaci gaba da faduwa dan hankalinta atashe yake,

Koda ya shigo wanka yayi sannan yayi sallah ya rokama matarsa da kuma bbynsa lafiya.
Yana saman sallaya,

Tana turo dakin da sallama ta zauna bakin gado.

Lokacin daya gama ya juya yana kallanta itama shi take kallan.

"Amma Fahad kasan yau Nike da girki amma kalli tym din da ka shigo gidan nan"

Kasa mata magana yayi kallanta kawai yake sannan yace "ina kikaje yau?" ya wurga mata wannan tamabayr lokaci daya.

Kamar zatayi karya ta dake tare da fadin "Gida naje mama bata jin ddi"

"Kinga irintah ko,saboda baki da hankali bakisan ciwan kanki bah,bakisan darajar aure bah,duk lokacin da kika ga damar fita saiki fitah,inda kina gidan ai zakisan abunda ya faru,dan kishi kin maida kanki marar tunani an shigo har cikin gida za'a kashe Sapna Allah ya taimaka da kwanan tah agaba"

Da sauri ta dago da kanta sannan ta kuma daure fuska tare da fadin "Kabani ajjiyar matar Kane fahad,ko akaina take zakazo kana gayamin magana akan  Wata er...'

Kafin ta karasa ya kwasheta da mari sannan ya kuma kara mata,Fitarmin daga daki jaka kawai,kinji kunya wlh.

 fashewa tayi da kuka tare da fadin "Fahad nika Mara,akan abunda ban sanibah,Allah ya isa Wallahi ban yafe bah"

Kamar ya shaketa ta mutu haka yaji dan xuciyarshi kamar zata Faso kirjinta dan bugunda take "kije na sakeki saki daya" sannan ya juya yabar mata dakin.

Hannu ta Dora aka tare da fashewa da kuka,Wallahi ban yafe bah,akan abunda ban sanibah zaka dakeni,harda saki.sannan taci gaba da kukantah.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Kamal dukkan abunda ya faru akan Sapna yasan dashi sabo da hakan yanajin kamar ya mutu,har asibitin yaje kuma ya samu lbrn ta farfado,da wannan ya ji ddi yana tunanin zai samu damar dazai dauketa ya kaita waje dan ta samu cikakkiyar kulawa.





😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer😘*
[24/3 23:31] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                 🌳
    *MARAICHI*❣
            *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
     *(Zeenaseer😘)*



8⃣2⃣





*••••••••••*Falo Fahad ya koma ya zauna,yama rasa abunda ke masa dadi ga abunda Mum tayi masa.

Har aka kira sallah asbah yana zauna yana faman tunane tunane,masallaci ya fita dan yin sallar.


*★★*
Salma kuwa data gama   kukanta tashi tayi ta koma dakinta,itama yanda Fahad beyi bacci bah haka itama batayi bah.
   Tasha kuka harta godema Allah, dan gani take Fahad ya cucetah,shekara da shekaru suna tare amma yanzu sabo da yayi saban aure harya daga hannu ya bigeta harda saki kuma.
   Shine abunda yafi daga mata hankali kenan.

Gari na fara haske ta shiga hada kayanta cikin trolley dinta ta yi wanka ta shirya sannan ta fito daga cikin gidan misalin *7:43am*,tana saka kayan nata cikin motah shima ya shigo cikin gidan,ko kallan inda take beyibah yayi shigewarsa cikin gidan.

Binshi tayi da kallo har hawaye na bin fuskarta.

Shiga cikin motar tayi taja tabar cikin gidan.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Mum bayan ta idar da sallah,zama tayi tayita yima Sapna addu'a Allah ya tashi kafadunta ya bata lafiya amma har lokacin Sapna bata farka bah.

*★★*
*8:13am* lokacin su Mum,Hajiya,Zee da Shaheeda suka iso cikin asibitin.

Kai tsayi dakin da aka kai Mum inda ya kasance kamar falone cikin dakin da Sapna take,da kujeru da toilet cikinsa,sai kuma kofar dakin da Sapnar ke ciki.

Tana zaune har lokacin tana lazumi,suka turo kofar dakin da sallama.

Cike da fara'a ta amsa musu sallamar sannan suka zauna aka gaggaisa.

Sun shigo da abinci kala kala da ruwar roba da kuma juice.

Nan Zee da Shaheeda suka jera cikin fridge sannan aka ajje basket da aka zubo flask din abincan.

Hajiya ce tace da Mum "Yame jikin?"

"Toh jiki da sauki za'a ce dan haryanzu ban gantaba kuma da alama bata farka bah.

" Allah de ya bata lafiya"Hajiya ta fada.

"Ameen" duk kuwa ya amsa.

*★★*
Fahad ma bayan Salma ta tafi wanka yayi ya shirya ya nufi asibitin.

Koda ya isa kasa shiga dakin yayi dan yana tunanin kar Mum tayi masa fada.

Ganin likitan zai shigone ya sanya suka gaisa abakin kofar sannan suka shiga tare.

Bayan sun amsa Musa sallama sannan suka gaisa banda Mum da taki amsa gaisuwar Fahad.

Likitanne ya shiga dakin da Sapna ke ciki,Shikuwa Fahad na zaune kan daya daga cikin kujerun.

Mamah ce tace da Fahad "be kamata kaki zuwa office dinka bah,ka tashi ka tafi dan sauki na Allah ne kaji bari a zuba ma abinci kayi breakfast"

Be mata musu bah yace "Insha Allah mamah zan tafi,amma na koshi nayi breakfast Nagode"

Mum de tana jinsu bata saka musu baki bah.

Bayan en lokuta kadan likitan ya fito daga dakin "Alhmdullh jiki da sauki amma har yanzu bata farka bah,in ganin ko allurar da aka matane yasanya saide zuwa anjima amma zaku iya ganin tah"

"Toh Dr.mun gode fah Allah ya biyaka" Hajiya ta fada.

Dukkansu suka mike suka shiga banda Fahad daya bari su fito sannan ya shiga duk da yana da bukatar danintah sosai.

Da sallama suka shiga dakin ahankali.

Mamah ce ta matsa garetah tana kwance idantah a lumshe,da alama bacci take sanya take da Riga fara tas me taushi,hannun ta sanye da drip,ganta an gyara gashin an daureshi ta bayan sannan an nannade gashin da bandage, gefan bakintama yayi jah alamun an ji mata ciwo.

Shafa mata kanta tayi tana ganin yarinyar tatah yanda ta zama babba harda cikin jikanta ajikintah,saide gatana a kwance kamar bazata tashi bah.

Kukane ya taho mata kasa daurewa tayi ta fita daga dakin haka Shaheeda mah.

Zee,Mum da Hajiya ne suka Dada dubata tare da mata addu'a sannan suka fito.

Zama sukayi suna kara bama mamah hakuri itama Shaheeda kukan take.

Bayan sun fito Fahad ya shiga dakin tare da matsawa gareta ya zauna kan kujerar kusa da gadan yana kallan kyakkyawar fuskarta.

Hannu yakai ya shafa mata kai sannan ya kamo hannun tah ya hada da nashi yayi mah hannun nata kiss tare da Dora wa kan fuskarsa.

"Soulmate" ya kirayi sunan tah ahankali "Allah Ubangiji ya baki lafiya insha Allah bazaki mutu bah zaki tashi ki Haifa mana bbynmu,muyi masa wasa mu René shi tare kinji,karki tafi ki barni dan Allah matatah,inasan ki banasan mu rabu har abada duk da watarana dole ne mu rabun.
I Lov you kinji,hawaye suka zubo masa yasa sannu ta dake rike dashi yana goge hawayn nasa.

Itama hawayan ke bun gefan idanta zuwa wajan kunan tah.

Mikewa yayi sannan ya manna matah kiss a baki da kuma cikinta sannan ya fitah.

Sallama yayi musu sannan ya fitah daga dakin yana tunanin soulmate dinsah.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Lokacin da Salma ta karaso cikin gidan nasu tunda taga motar Abbantah gabanta ya fara faduwa dan tasan halin sa baya saurara mata.

Bayan tayi parking motar,ta fito da kayanta ta nufi kofar shiga cikin gidan.

Da sallama ta shiga cikin falon nasu.

Aikuwa Abban na falo shiya amsa matah sallamar yana zaune yana kallan news.

Gabantane yayi mugun faduwa,mamantah na kitchen.

Ahankali ta karaso cikin falon tare da durkusawa.
" Abba ina kwana"

"Lafiya" ya masa yana matah kallan tuhumah.

"Daga ina kike" ya warga matah wannan tambayar.

"Daga gida nake Abba" ta bashi amsa kanta a kasa.

"Karya kike menene ya kawoki a wannan lokacin" ya fada

"Abba dama mm..Fahad dinne ya sakeni"

"Uhmm dan Halak kenan dama wannan ranar nake jira gata Allah ya nunamin,burinki ya cika ko Salamatu?"

Shiru tayi tana hawaye.
Mamah dake kitchen taji kamar magana yasa ta fito ganin Salma yasatah kara matsowa tare da fadin "Lafiya Salma da Safiya haka?"

Abba ne yaci gaba "Saikizo ki zauna agidan tunda kin kasa zaman auran dama nasan watarana saiya sako ki"

"Saki kuma" Mamah ta maimaitah "sakinki Fahad din yayi?" Ta kuma tambaya.

Daga kanta tayi alamun "eh"

"Haba Babansu me makon ka kirashi akanme zai sakar maka er kah amma saika fara matah maganganu haka kamar maras gata,in kai bakasantah ni zan je har gidansu"

Kallanta yayi tare da fadin "wlh ko karan wani nasa kikakyi a waya ba zuwaba kema abakin naki auran" yana kaiwa nan yabar falon..









😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷







*Written by Zeenaseer😘*
[24/3 23:31] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳         ⚜      🌳🌳
🌳                              🌳
                 👑👑
                    🌳
       *MARAICHI*
               *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
      *(Zeenaseer😘)*



8⃣3⃣


*Dedication to sis Hamagee🙌🏻❤😘*




⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
*•••••••••••*Hankali mama ta dagota daga ta suka zauna saman kujera tana kallanatah.
  "Haba Salma garin yaya kika bari wannan abu ya faru haka kinsan yaran nan yana da hakuri ba mamaki makura kika kaishi"

Kuka taci gaba dayi tare da fadin "Wallahi mama kawai dan yayi saban aurene"

"Aa fah nima kaina bazan mai shedar hakan bah,yana sanki Fahad amma bakimai biyayya yanda ya kamata Salma yanzu me gari ya waya,gashi kin je an cire miki mahaifa yanzu kinga ai matarshi ta dinga haifamai yara kinga kuwa dole yana rawar kafa kanta da yaranta"

Kuka sosai take yi.

"Tashi ki tafi daki ki zauna,kinga gashi babanku ya hana ayi wani Abu da dakai na zanje na samu mahaifiyarsa,amma asan abunyi Allah ya kiyaye"

Mikewa tayi taja trolley dinta ta nufi dakin su tana share hawaye.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Daidai kofar asibitin Kamal yayi parking ga motarsa ya fito.
   Sanya yake cikin manyan kaya sunyi masa kyau sosai.
   Cikin takunsa na kasaita yake shigowa cikin asibitin harya karas ciki wajan office din Dr.
   Ahankali ya shiga knocking kofar.

Bashi izinin shiga akayi sannan ya tura ya shiga tare da zama bisa kujerar dake kallan ta Dr.
   Hannu Dr.ya mika masa suka gaisa sannan ya ce dashi "barka da zuwa"

"Yawwa" Kamal yace dashi kafin yace nasan baka gane ni bah kokuma ince bama ka Sanni bah gaba daya"

"Hakane" Dr.ya fada.

"Wato Dr.wata magana ce me amfani ko kuma ince maka wani aiki nakesan muyi nida kai"

Shiru yayi yana kallansa kafin yace "wani aiki kenan?"

"Ywwa,nasan Kaine kake kula da patient Sapna wanda aka cakama huka tana da ciki kuma matar fahad kenan"

"Hakane tabbas nine likitan su"

"Masha Allah, Dr.zamu zo yau misalin karfe *1:00am* daidai zuwa *1:40am* zamu bar kasar nan da itah"

Kallan shi kawai Dr.yake kafun yace"kana da hankali kuwa,tun kafin ranka ya bace ka fitar min daga office "ya mike tsaye yana magana cikin bacin rai.

" calm down, calm down Dr, zan baka zabi gudu biyu ba sai munkai ga haka bah,na farko ko ka yarda kokuma da dauke er ka dake makarantah *ss2*wato saudat ko kuma nabaka *5million's naira*zabi ya rage nakah.

Shiru likita yayi yana nazari kafin yace "dan Allah me yasa kake san sakani cikin tashin hankali kusan shekara *20*ina aikina cikin kwanciyar hankali amma yanzu zaka batamin aikina meyasa haka dan Allah.

" Dr.naga kamar kana batamin  lokacina kawai ka bani account numb.dinka"

"Gaskiya bazan iyaba saide kazo kaya yanda zakayi amma ni bazan amshi kudin kaba kuma karka taba min yarinya tah" Nagode.

Shikenan "inasan kayi mata allurar da bazata barka ba ta kamar tsawan 10hrs"

"Babu damuwa Allah ya bada sa'a zanyi matah"

Mika masa hannu Kamal ya kumayi suka gaisa sannan ya fita daga office din.

Ajjiyar zuciya likitan yayi dan yaga abunda yafi karfinsa.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Dakin ya cika da mutane en dubiya har en katsina da Aisha duk sunxo,kowa na jajin tawa,Aunty Rahma mah gobe tace tana tafe.

Kowa sai mamakin yanda wannan Abu ya faru haka yake,taya za'a shigo har cikin gdn ga me gadi,toh ba shima da amfani kenan.
   Aisha ce tace "ni Wallahi Salma nake zargi"

Hajiya ce tace "Aa bade asan koma waye bah kuma komin daran dadewa Allah zai tona asirin koma waya Allah bama Sapna lafiya de ya kuma sauketa lafiya"

"Ameen suka amsa har Maman zee itama tana nan.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Salma na zaune kan gadanta ta rasa abunda ke mata dadi duk duniya tama rasa yanda zatayi taji dadi,wayr tace tayi ringing, ahankali ta janyo ta daga tare da karawa a kunnan tah dan tasan Safiya ce ke kira.

" hello! Salma kina inane nazo gida bakyanan kuma gashi inasan magana dake"

"Safiya ina gidan mu kizo nan kawai"

"Ok! Gani nan zuwa" sannan ta katse kiran.

*★★*
Lokacin data karaso tayi parking din motar ta sannan ta fito ta shiga cikin gidan.

Da sallama ta tura kofar dakin.

Mamace zaune tana karatu babu kowa a falon.

Amsa mata sallamar tayi sannan ta karaso ta zauna tare da gaidata.

Bayan ta amsa mata tace "bari na taso miki Salman.

Sannan ta mike ta kirata ta hada mata da juice ta kaima tah.

Jikinta a sanyaye ta shigo cikin falon.

Ajje mata tray din data dauko juice da cup din tayi saman centre table sannan itama ta zauna.

Kallanta Safiya tayi tare da fadin " lafiya kuwa Salma naga fuskarki dama yanayinki duk sun canza?"tana magana tana tsiyaya juice din cikin cup sannan ta dauka takai baki.

"Safiya Fahad ya sakeni"

Batasan lokacin datayi tqri bah leman bakinta ya zubo bah 😳"ya sakeki fah kikace?"

Shiru tayi kafin tace "wlh tun daran jiya.

Matsowa ta kumayi kusa da ita sannan tayi kasa da muryartah " bade ya gano mubah?

"Ko daya fada mukayi dashi"

"Haba kema garin yaya kuma"

"Sapna fah bata mutu bah kike hau kanki"

😳"Tashin hankali,tana wani asibitin?"ta kuma tambayarta.

"General hsptl mana shine asibitin mu"

"Amma kai yanzu yama zamuyi ai in bata mutu bah munshiga uku,Wallahi Salma mundun Sapna ta furta mata ne suka mata wannan aika aikan dama babu wanda za'a zarga sai keh"

Kamar zatayi kuka tace "toh yanxu ya zanyi,Abba ba barina fita zaiyi bah"

"Kinga na miki alkawarin daran yau da hannuna zan kashe Sapna, kawai abunda nakeso dake koma me za'ai kada wani yasan sirrinmu kinji?"

"Insha Allah Nagode Safiya" ta fada tare rungumeta.

Mikewa tayi tare da "fadin bara naje zankiraki,kuma zaki koma gidanki"

Salma taji ddi sosai dan Safiya na mugun santah.

Har wajan motar ta ta rakata sannan ta fita.

Har ta kusa kaiwa bakin kofa zata shiga gida Abba ya kirata.

Jiki a sanyaye ta karawa gabansa tare da durkusawa.
"Abba gani" ta fada kanta a kasa"

"Wace waccan yarinyar?"

"Am...h. Abba kawatace"

"Karna kara ganin wata da sunan kawarki acikin gidana kinji na gaya miki"

"Toh insha Allah"

"Tashi ki bani waje"

Sannan ta mike tare da shiga ciki.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Bayan sallar la'asr, Dr.ya shiga cikin dakin da Sapna take dan yimata allurar bacci kamar yanda Kamal ya umarceshi.

Yana tura kofar dakin,ya tsaya yana kallanta cike da tausayintah.

Ahankali take bude idanunta da take gani fishi dashi sun cika da ruwa.
  Ganin ta kasa tsaidasu ya sanyata maidawa ta lumshe su nan da nan ruwan ya zubo kan kumatunta.

Haka Dr.ya kama hannunta tare da yi mata allurar sannan ya fita daga dakin.

Ba jimawa ta koma baccin da takeyi.

*★★*
Bayan magariba Dad na zaune cikin asibitin dan yazo duba Sapnar sa.
  Yaji dadi sosai da ganin dangin Sapna sunata mai godiya da irin rukwan da yayima tah.
  Nan ya nuna akan zai fita da ita abroad dan akuma dubata amma Hajiya tace abarta anan kawai sauki daga Allah yake koma aina ne .

Dad ne ya kuma cewa "amma wannan wani irin abune ace tun jiya amma har yanzu bata farka wani irin bacci ne wannan"

Kowade shiru yayi sai fada yake faman yi.

Da sallama Fahad ya turo kofar dakin.

Bayan sun kuma gaisawa da jama'a suka kara masa jaje.

Dad ne ya kuma cewa"Fahad yarinyar nan canza mata asibiti zanyi"

"Toh Dad nima yanzu na gama tunanin hakan"

"Ywwa sai kama Dr.magana dan ayau nakesan canza matah"

Mikewa yayi tare da fadin "toh Dad bara naga Dr.din"

Sannan ya fita daga dakin.






😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer😘*
[24/3 23:31] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳       ⚜        🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                 🌳       
    *MARAICHI*❣
            *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
     *(Zeenaseer😘)*




8⃣4⃣




*•••••••••••••*Fahad yana fita office din likitan ya shiga bayan sun gaisa ya ke sanar masa bukatar Dad din.

Shiru Dr.yayi nadan lokaci kafin yace "Amma Fahad ya zakuyi haka,kasan kai tamkar aboki kake agurina kuma asibitoci da yawa basu amsar patient da irin wannan case din amma haka na amshi matarka mukayi mata abunda ya dace kuma lokaci daya kuce zaku tafi kaya hakuri mana sauki na Allah ne koma ina kukaje"

Fahad ne ya dafa hannun Dr.tare da fadin ba laifina bane laifin Dad ne saide kamai bayani da kanka danni koda nayi mai ba zai yarda bah.

Shiru ya kuma yayi kafin yace "muje toh mugani ko zai amince"

Tare suka fito daga office din,sannan Fahad yayima Dad magana bayan ya fito suka gaisa da Dr.sannan Dr.yace "Amma dan Allah Ku barta anan mana muna bata kulawa yanda ya kamata am..."

"Dakata da Allah Dr."
Dad ya dakatar da shi.

"Ni banan asibitin nayi niyar kawo yarinya ba ya dauketa ya kawo ta nan sabo da haka zan dauketah daga nan,na gaya makane dan babu ddi kaga bama nan ko kuma da kudin ka wajan mu"

Dr.shiru ya kumayi sannan yace "babu ko Sisi da muke bunku,Allah ya bata lafiya" yana kaiwa nan ya juya ya tafi.

Nan take Dad ya dauko wayarsa ya kira babban abokinsa Dr.shehu inda za'a kai Sapna.

Nan kuwa ya amsawa Dad daya kawotan dan ya gama shirin amsartah tunda tun jiya sukayi maganar da Dad din.

Nan kuwa aka saka nurse suka daukota aka sakata cikin motah sannan en gida suka hada nasu ya nasu suka bar asibitin kafin *12am* Nan danan suka isa *International hospital*
Dayake dama ansan da zuwan su nan danan aka amsheta aka basu daki me kyau komai na asibitin a tsare yake gwanin ban sha'awa.
   Bayan duk sunga asibitin da kuma dakin da aka kwantar da itah sannan Dad yasa aka sanya security awajan corridor dakin har waje.
  Duk wanda zai shiga dakin sai an duba shi mundin baka sanye da kayan likitoci.

Bayan nan aka maida kuwa gida yau ba Mum bace ta kwana wajan tah Hajiya da Shaheeda aka bari sauran suka tafi gida.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Tunda aka dauke Sapna daga asibitin Dr.ya kasa zaune ya kasa tsaye dan hankalinsa atashe yake besan me zaice da Kamal bah.

Yana san ya kira shi amma kuma yana jin tsoran abunda zai faru.

Yana zaune kan kujerar sah har bacci ya fara daukarsa yana tangadi!

Wayar shice tayi kara,a firgice ya mike zaune tare da daga kiran dan yasan bazai huce Kamal ba.

Daga wa yayi tare da sallama.

Batare daya amsa masa sallamar tasa bah ya ce dashi "Taya zaka bari a dauke Sapna daga asibitin kah,amanatah kake san ci kenan ko?"

"Dakatah Kamal ni bani na saka hakan ta faru bah,su sukace zasu canza mata asibiti nikuma ban isa na hana suba kaji abunda ya saka"

Tsaki yaja sannan ya kashe wayar.

Wata ajjiyar zuciya Dr.ya ajje dan ba karamin dadin hakan yaji bah sai yanzu yaji dadin jikinsa.

*★★*
Bayan tafiyar su Sapna, Safiya ta karaso cikin asibitin itama.
   Lokacin data isa reception ta tambaya ko akwai wata patient mai suna Sapna da aka kawo jiya.

Dubawa receptionist din tayi sannan tayi mata kwatancan dakin.

Kai tsaye ta nufi dakin ta tura amma a kulle hakan yasa ta tsaya tana mamakin yanda taji dakin akulle.

Daidai dakin ta tsaya lokacin Dr.yana fitowa daga office dinsa.

Ganin mace awajan kofar ya sashi kara sowa tare da fadin "lafiya baiwar Allah ko kina neman wani abunne?"

"Ywwa ina yini"

"Lafiya qlau" ya amsa.

"Dama ina neman er uwatane Sapna da aka kwantar anan asibitin"

"Eh toh zai iya yiyuwa basu sanar dake cewa basu dade da canza mata asibiti"

Gabantane ya fadi Amma bata nuna masa bah "tohhh! Toh da Allah kasan asibitin da aka maidatan kuwa?"

"Gaskiya ban sanibah saide ki kara ki tambayesu"

Toh nagode sannan ta juya ta fita.

Tana fita ta kira Salma a waya.

*★★*
Ita kuwa Salma ta kasa bacci kawai jira take Safiya ta kirata ta sanar matah yanda akayi.

Tana kwance taji kiran ya shigo wayar tatah.
  Da sauri ta mike tare da dagawa ta kara a kunne.

Safiya ce tace da ita "keh Wallahi naje asibitin wai anjanza mata asibiti"

Gyara zama tayi cike da mamaki "toh ya haka ta faru,wani asibitin suka kaita kode an ganu mune"

"Toh wallah nima ban Sani bah, saide yanzu ta inama zamu fara neman su"

"Ki kara Fahad mana"

"Gaskiya baki da hankali Safiya, tayama zakice na kira Fahad Wallahi bazai daga bah"

"Kinga kawai saida safe ma hadu sai musan abunyi kawai"

"Toh shikenan,saida safe"

Sannan ta kashe wayar.
  Gyara zama tayi saman gado tare dayin Uban tagumi tana tunanin inda aka kai Sapna, gashi batasan ta inda zata fara bah,Abba ya hanata fitah haka ya hana zuwa kuwa gurin tah.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Yana zaune acikin club yanata bankar giya koya samu nutsuwa dan kanshi yayi mugun daurewa.
   Kwalabe rututu agaban sa,yasha iya shansa,da ker yake iya bude idansa daya kada yayi jajir.
  Sannan hannun sa daya rike da cigarette yana busawa.

Bash ne zaune a gefansa yana kallo waya.

Bayan ya gama ne ya amshi cigarette dake hannun Kamal ya cigaba da sha.
   Juyawa yayi ya kalli Kamal ganin duk ya fita haiyacinsa yasan duk maganar da zasuyi bazai gane bah.
   Mikewa yayi tare da janshi zuwa cikin mota sannan suka tafi gida.

Suna cikin tafiya ya canza hanyar daba ta gidan ya kamata yayi bah.

Wayar shi ya fito da ita sannan ya dailing wata number ya kira.

Bata jima da fara ringing bah aka dauka.

"Hello!" ya fada

Daga dayan bangaran aka amsa.

Sannan ya furta ina daidai inda mukayi daku Ku karaso sannan yayi parking motar awajan.
 
Ahankali ya dauko wata karamar allura ya caka ma Kamal a huyansa sannan ya cillata ta window jin zafin dan yayi a yuyansa yasa ya zabura tare da buge Bash har saida bakinsa ya fashe.
   Fitowa yayi daga cikin motar tare da kulle shi aciki,ya gama bige bigensa sannan ya suma awajan.

Bayan kamar 5mins da tsayiwarsu awajan.
  Mayan motoci suka karaso wajan gudu 3,bayan sunyi parking, daya daga cikin mota ta farko ya fito tare da bude gidan baya a mota ta tsakiyar wato ta 2.
  Wani babban mutunne ya fito daga cikin motar fuskarsa ba annuri ya mikama Bash hannu suka gaisa sannan ya nuna musu motar tare da fadin "yana ciki"

Mutuminne ya saka aka dauko Kamal aka sakashi cikin motar sannan aka dauko wasu akwatina gida 3 cike suke da kudi aka mika masa shima ya sakaso acikin motarsa sukayi sallama da mutanan ya tafi.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Bayan Safiya ta koma gida tana shiga ta tura kofar dakin ta kulle tare da zama kan kujera dan itama kanta a daure yake.
   Cike da mamaki dan tadan turata,da ganin Bash zaune yana Murmushi da kwalbar giya a hannunsa yana sha.
  Mikewa tayi tare da karasawa gareshi tana kallan manyan akwatinan dake gabansa cike da kudi.

"Bash wannan fah da nake gani haka?"
Ta tambayeshi tare da zama tana taba kudin.

Murmushi yayi sannan yace "mutumin naki ya tafi wannan ladan ne aka bani"

"Amma ban fah gane abunda kake nufi bah"

😸😸😸dariya yayi tare da mikewa tsaye ya isa bakin window sannan ya fara mata magana "Leon shine ogan Kamal wajan aikin da yake,ya sanya makudan kudi da kuma karin girma ga duk mutumin daya samu damar kawo masa Kamal araye,sannan ya da da kurbar giyar kafin ya kuma cewa " Nikuma na samu nasarar bada shi saka makun daya daga cikin en kungiyar daya bani aiki"
   Wannan shine ladan dana samu.

"Wani uban ihu Safiya tayi tare da rugowa ta rungume Bash ta baya " gaskiya naji dadi dama ina neman hanyar dazanbine dan kawar da Kamal dan cikar soyayyar mu sai kuma gashi yau burina ya cika"
   Juyowa yayi tare da kuma rungumetah "Masoyiyatah nabaki kaso daya cikin kudin nan"
Wani ihun dadin ta kumayi tare da kara kankame shi,sannan ta warce jiyar hannun nasa ta rufe idanta tare da kwankwada.
   Sannan ta shiga kissing Bash nan suka shiga bidalar da suka Sabah.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Bayan Dr.shehu ya gama duba Sapna yanda ya kamata sannan ya shaidama su Fahad cewa zata farka nan da shafiya insha Allah sakamakon allurar baccin da aka matane.

Dan sai kusan *2am* Fahad yabar asibitin.






😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer😘*
[24/3 23:31] Hussaina: *©ECQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
                👑👑
                   🌳
       *MARAICHI*❣
                 *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
      *(Zeenaseer😘)*




8⃣5⃣





*•••••••••••*Washe gari da safe Misalin *8am* Su Mum suka isa asibitin da sallama ta tura kofar dakin.
   Bayan sun amsa sallamar suka gaisa sannan ta ajje abincin da ta kawo.
   Bata jima da zuwa bah su Mamah da en katsina suka shigo.
   Nan danan mutane suka fara taruwa.


Da yake weekend ne Fahad bashi da office shima da huri yazo sannan Dad shima ya iso.

*★★*
Zaune suke cikin dakin anata faman hira.
   Fahad na zaune a gefe yana danna wayar sa.

Dad da Dr.Shehu, bayan sun gaisa da mutanan sannan ya fita ya nufi dakin da aka kwantar da Sapna shikuma Dad ya zauna wajan mutanan.


Yana shiga dakin ya duba jikin nata,ahankali ta fara motsi da hannu ta,dan ya hana ko wata nurse ko Dr.ya dubata in ba shi kadai bah.
   Tun tana kin bude idan nata har ta bude shi gaba daya.
  Akan Dr.ta sauke su sannan ta rinka bin dakin da kallo.

"Sannu Dr.yayi mata"

Batare da ta bashi amsa bah ta lumshe idanuntah.

Allura ya kara mata sannan ya juna mata saban drip din.

Tana san ta ce tana da bukatar ruwa amma bakinta yayi mata nauyi.

Bayan Dr.ya fita daga dakin kai tsaye dakin da su Mum suke ya shiga da Murmushi a fuskar sah.

"Alhmdullh saide aci gaba da yima ta addu'a Allah ya sa ta farka"

Kowa hamdala ya shiga yi da godiya ma Allah.

Yanzu zaku iya shiga Ku gantan babu matsala.

Alhmdullh suka fara fada dan farin ciki.

Shaheeda ce ta fara tashi da sauri ta bude dakin dan har kuka dadi ta fara.

Ahankali ta tura dakin da Sapnar ke a kwance da sallama ta shiga tana kallanta kwance kan gadan.

Jin anyi sallamane ya sanyata,bude idanta Amma ta kasa juya kanta.

Zagayawa dai dai fuskarta Shaheeda tayi tana Murmushi da kwallah a idan tah.

Tana isa daidai ita ta dan durkuso tare da dafa kanta murya na rawa tace "ya Sapna sannu"

Binta tayi da kallo tana tunanin inda tasan fuskarta tah.
  Cikin karfin hali ta furta "Shh..Shaheeda"

Girgirza mata kai take yi tana hawaye "eh ..eh nice ya Sapna nice"

Rungumeta tayi tana kukan itama hawayan take dan bazata iya kuka me karfi bah saka makwon ciwan da cikinta ke matah.

Da sallama su Mama suka shigo Amma banda mazan.

Hajiya ce ta janye jikin Shaheeda daga na Sapna tare da fadin "Ya isa haka Ku barta ta huta tukun.

Kuka shabe shabe a fuskarta idanta har yayi jah,murna fal cikin zuciyarta jitake kamar ta tashi ta yi murnar da tafi wannan.

Ahankali Mama ta fito daga bayan Hajiya itama kukan take ga kuma fuskarta dauke da Murmushi.

Sapna ganin Maman tah gabanta ya sanyata Binta da kallo tana kokarin tashi da sauri Maman ta maidata ta kwanta tana girgiza mata kai " kwanta kinji Allah ya baki lafiya Sapna nice mamakin Allah ya bani lafiya Sapna, Allah ya sauke ki lafiya.

"Ma..mah..mamah,mamamu kece"

Itama rungumeta tayi tana kukan,lumshe idanunta tayi tana jin dumin jikin mamantah wanda raban data jishi harta mantah.

Ta jima rungume ajikintah sannan taja baya badan Sapna taso haka bah.

Daya bayan daya ta rinka ganin mutane,farin cikin da take ciki bazai iya fallasuwa bah,banda kuka babu abunda takeyi.
  Dr.Shehu ne su fita su barta tadan huta tukun be kamata daga tashinta tqfara kuka haka bah.

Haka duk suka fita sannan Dad da Fahad suka shigo cikin dakin.
  Bayan Dad ya dubata sannan shima ya fita Fahad kawai aka bari cikin dakin.

Ahankali ya zauna kusa da ita tare da rungume ta shima,itama hannun ta tasaka ta rike shi.

"Sannu soulmate ya fada yana ajikintah"

Shiru tayi tana jinshi,kafin tace " Hubby inajin yinwa kuma inajin kishirwa"

Ahankali ya janye jikinsa daga nata sannan ya shiga goge mata hawayan fuskarta, "ki dena kukan ya isa haka kinji"

Gyada masa kai tayi alamun toh.

"Ywwa bara na tambaya ko za'a iya baki wani abun" sannan ya mike tare da bata peck agoshi ya fita daga dakin"

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Lokacin da mutanan nan suka tafi da Kamal wani tsohon gida suka nufah dashi bayan duk sun kwashe mai wayoyinsa da duk wani Abu na amfani ajikinsa.

Yana  da safe ahankali ya bude idansa sannan yayi maza ya mike zaune tare da dafe kansa dayake bara zanar tsagewa.

Kallan dakin ya shiga yi ahankali ya ringa tuna abunda ya faru daran jiya,hannunsa yakai daidai huyansa inda Bash ya cakamai allura.
   "Auach" yadanyi kara jin gurin still yana masa ciwo.

Saukowa yayi daga saman gadan yanata kallan dakin.
Babban dakine da gado da wardrobe da kuma toilet acikinsa,sai kuma kayan kallo a gefe da karamin fridge wanda yake cike da giya da ruwa da kuma lemo,
Dakin yana da kyau kana ganinsa kaga na masu kudi.
  Wata iriyar kofa dakin gareshi wanda duk bala'in kutun be isaya ya bude tabah wanda Cord ma ke gareta sai kuma fingerprint.
   Gaba daya ya ma rasa yanda zai fassara abunda tabbas Bash yaudarar yayi,wayema yasa akawosa dakin nan kenan taya taya,ya kurma uban ihu tare da fadawa kan gadan.

Wayr dake kusa dashi ya dauko jin tana ringing ahankali ya kara a kunne.

Dariya aka farayi kafin daga can bangaran ace "kai karamin yarone har yanzu bakasan rayuwa bah,nasan kana cikin rudani toh haka zaka kasance har abada,kanaji kana gani za'a kaika  har gaban Leon ya dauki mataki akan ka mukuwa dukiyace tamu" ya karashe maganar yana dariyarsa sannan ya kashe wayar.
   Binta yayi da kallo kafin ya dagata sama ya hadata da bango nan da nan ta tarwatse.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Washe gari da safe Salma da ciwon karya ta tashi dan Abba ya barta ta tafi asibiti dan su hadu da Safiya.

Lokacin da Mamah ta gayama Abba abunda ke damuntah, Abba cewa yayi bari yayima likitan sa waya kozai samu damar zuwa ya dubata.

Kokadan bataji dadin hakan bah.
Kamar zatayi kuka.

Amma likitan yace baya gari bazai samu damar zuwa ba,saide taje asibiti.

Haka kuwa yace ta shirya taje asibitin sannan ta kawo masa komai da akayi a receipt din yagani.

Sannan ta fita daga gidan ya kuma bata kudin napep dan ya hanata hawa motar tatah.

Lokacin data fito daga gida babu kudi a wayarta tana tarar Napep gidan Safiya ta nufah.

*★★*
Safiya ta samu kudi sai murna fal cikin tah dan Bash ya tsaya matah.
   Tana kwance da safe bayan tagama breakfast Bash kuwa na daki a kwance shima abinshi.

*9:13am*
Daidai Napep yayi parking kofar gidan Safiya.
  Dayake megadin ya santa nan danan ya bude mata kofar ta shigo.

Safiya na falo taji an turo kofa,da sauri ta mike zaune ganin Salma ce ke shigowa.

Zama tayi kan kujera tare da fadin "keh Banga ta zama bah ya zamuyi kenan kinsan da er na fito daga gida ko mota babu kuma Abba yace karna jima"

"Hakane Amma ta ina zamu fara yanzu ko gidan su Fahad zamuje mu tambaya asibitin da aka kaitah"

"Eh hakane kin kawo shawara bari na shirya" sannan ta mike ta shiga daki.

Bayan ta shiga daki Bash ya fito sanye da gajeran wando da singlet fara ajikinsa.

Tunda yaga Salma ya kura mata Ido dama Mayan matane.

Ita kuwa a tunanin tah shine mijin Safiya tunda bata taba ganin Kamal bah "ina kwana" ta gaida shi

"Lafiya qlau" ya fada yana kallanta.

Ita kuwa cigaba tayi da danna wayarta dan batama san yana yibah,

"Ina Safiyar take ne"

Batare data kalleshibah ta ce dashi "eh ta shiga ciki yanzu ba jimawa"

"OK!" Ya fada sannan ya juya ya shiga cikin dakin da Safiya ta shiga.

Tare suka fito shida ita sannan tace da ita "Salma mu huce mana"

"Sannan Salma ta mike ta fita"

Safiya ce ta kalli Bash tare da fadin "Saina dawo" ta fita ta barshi Shikuwa hankalinsa nakan Salma.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Fahad wajan Dr.Shehu ya nufa wato office dinsa.
  Bayan ya shiga ya tambayeshi "ko za'a iya bama Sapna ruwa da abinci dan tanajin yinwa"

"Eh za'a iya bata Amma ya kasance liquid kamar custard ko kamu,Amma kar abata ruwa"

"OK" ya fada sannan yabar dakin.

Dakin su Mum ya nufa ya sanar musu da abunda Sapna ke bukata nan danan akace yaje ya siyo sai a dama matah.

Sannan ya fita dan zuwa ya siyo.






😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer😘*[24/3 23:31] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳         ⚜      🌳🌳
🌳                              🌳
                👑👑
                   🌳
       *MARAICHI*
               *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
     *(Zeenaseer😘)*




8⃣6⃣




*••••••••••*Bayan ya dawo daga siyan custard din aka dama mata sannan Fahad ya amsa dan ya bata.

Shiga dakin yayi sannan ya zauna kan kujerar da ke kusa da gadan natah.

"sannu soulmate" ya fada tare da dan gyara mata kwanciyar tatah yanda zataji dadin shan custard din.

Ahankali ya dinga hura mata yana bata saida tasha sosai ta koshi sannan ya barta haka.

Dr.Shehu ne ya shigo tare da magunguna tare da mikama Fahad kuma yayi masa bayanin yanda zai batah.

Nan take ya dauko ruwa sannan ya bata magungunan tasha duk da batasan shan magani.

Allura Dr.Shehu ya kara yi matah sannan yabar dakin.

Gyara mata bakinta yayi,sannan ya shiga toilet ya jiko wani karamin towel da ruwan dumi ya goggoge mata jikin nata sannan ya gyara mata kwanciyar yanda zataji dadi,

Kallanshi kawai take tana Murmushi yanda yake kulawa da itah,sanshi na dada shiga cikin zuciyarta.

Kallanta yayi tare da sakar matah Murmushi"ki kwanta ki huta kinji tawan" sannan yaja mata blanket din tare da manna matah peck a gashin tah "I Lov you soulmate"

"I Lov you too", ta fada tare da janyo yimai peck a hannunsa.

Sannan ya juya ya bar nakin tare da janyo mata kofar.

Lumshe idanta tayi tana Murmushi jin ddi,tabbas Allah shine abun godiya,daya kawo mata danginta farin cikinta da kuma ya bama mamanta lafiya,babu abunda ya kamata tayi sai godiya ga Allah daya bata miji me kaunar tah, tana wannan tunani har bacci barawo ya dauketah.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Lokacin dasu Salma suka isa gidan babu kowa me gadi ya sanar musu.

Safiyace ta tambayi me gadin tare da fadin " dan Allah Babah ko kasan inda Hajiya ta tafine"

"Eh taje asibiti ne inda aka kwantar da surukarta saka makwan wani hatsari data samu"

Dama ita Salma na cikin motah bata fito bah.

"Subhanallahi" Safiya ta fada "Allah ya bata lafiya,Baba ko kasan sunan asibitin da aka kaitah?"

"Eh gaskiya ban sanibah Amma bara na kira Hajiya sai na tambayetah"
Ya karasa maganar tare da dauko wayarsa daga cikin aljihunsa yayi dailing number ta bata jima tana ringing ba ta dauka.
   Bayan sun gaisa yake ce matah "Ranki ya dade dama baki kikayi kuma suna san a gaya musu sunan asibitin"

Shiru Mum tayi kafin tace "international ne hawa na biyu daki na 3"

Nan ya gayama Safiya yanda sukayi,sannan ta dan bashi wani abun tayi masa godiya ta juya ta koma motar.

Bayan ta shiga ta kullo Salma ta bita da kallo tare da fadin "kinji fah international hsptl ne second floor,room3"

"Shike nan mah,dama can zani inyaso tunda ke baki sansu bah sai kije kinga wajan ni sainaga likitan"

Haka suka yanke shawara sannan taja motar suka bar wajan.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Gaba daya Kamal baya jin dadin rayuwarsa ga rashin Sapna da yayi ga kuma kamashin da Leon yasa akayi,sai faman shan jiya yake yana fasa kwalaban yana haka shika dai cikin dakin.

Bacin yasha yayi tatul ya kwanta saman gadan yana shan iska.
Sai faman lumshe idanunsa yake har bacci ya dauke shi, duk abunda yake camera na kallansa.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Bayan Fahad ya fita daga dakin ba jimawa,Shaheeda ta taso ahankali ta shiga dakin da Sapnar take a kwance.
  Turawa tayi ta sameta har tayi bacci,zama tayi tare da kamo hannun tah tana kallan fuskar yayar tatah dan tana mugun san Sapna a rayiwarta.
   Ta jima a dakin sannan ta fito ta koma dakinsu.

Hajiya ce ta kalli Shaheeda tare da fadin "Shaheeda tashi ki fita ga Auntyn kucan Rahma ta iso itama ki shigo da itah.

Cike da murna ta mike cike da murna dan ta jima basu hadu bah,gashi har Daddy girmah.

Da sauri ta yafa veil din doguwar rigarta ta fita.


*★★*
Daidai lokacin Salma da Safiya suka fito daga cikin mota dan shiga asibitin.
   Zama sukayi a reception suna jiran Salma ta shiga wajan Dr.ita kuma ta shiga dakin da Sapna take.



Shaheeda na fita ta hango Aunty Rahma tsaye tana jiran su hannunta karamin yarone da lollipop a hannunsa yana sha.

Da sauri ta karasa tare da rungume tah tana murna.

Itama dariya take ganin yanda Shaheeda ta kuma girma ga kuma kyau data kara.

" ikon Allah Shaheeda en matah haka aka zama kice mun kusan zama sirikai"

Kunya ta danji tare da fadin "kai Anty,sannu da zuwa" sannan ta dauki Daddy.

"Laah! Anty kinga baya kiwa"

"Aiko nima nayi mamaki dan baya yarda da mutane sosai"

Haka suka shiga cikin asibitin suna hira.


Daidai lokacin Salma ta shiga ganin likitan.


Suna tafe suna hira Shaheeda nama Daddy wasa.

Daga kan da Safiya zatayi dan daga wayar da ake kiranta,idanta suka sauka akan Anty Rahma sunta faman Murmushi ita da Shaheeda.

Tsaye ta mike taci gaba da binsu da kallo baki bude.

Gaba daya ta sandare wajan zuciyarta ta shiga wasu wasi.

Da sauri ta rataye Jakarta ta shiga binsu abaya tana boyewa.

Har suka shiga lift.

Tana tsaye ganin inda zasu yasa tayi maza tahau dayar.

Daidai second floor suka tsaya haka itama,Amma da ta fito bata gansu bah ta duba gabas da yamma amma babu su.

Da sauri ta shiga nemansu dan ganin hanyar da sukayi,tabbas Anty Rahma ce wacce dayar kuma bata gane ko wace bah.

Jikinta har karkarwa yake ta shiga dailing number Umma.

Bata jima bah tana ringing ta dauka.

Tana faman nishi kamar wanda tayi tseran gudu tace da Umma "Umma ki duba mini dan Allah ko Anty Rahma na gida"

"Lafiya Safiya naji hankalinki atashe meya faru?"

"Dan Allah ki duba min mana"

"Safiya bata nan sunyi tafiya "

"Shikenan Umma, Umma naganta yanzu a bauchi kuma ina tunanin wajan Sapna tazo"

"Sapna kuma kina da hankali kuwa Safiya, me kuma zai kawo Rahmatu wajan Sapna, dakata mah wace Sapnar?"

Bata jira bawa Umma amsabah ta saka wayar cikin jaka batare data kashe bah.






😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer😘*
[24/3 23:31] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜       🌳🌳
🌳                              🌳
               👑👑
                 🌳
    *MARAICHI*❣
             *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
     *(Zeenaseer😘)*




8⃣7⃣





*•••••••••••*Cigaba tayi da dubawa amma bata gansu bah.
   Tana ta mamakin inda suka shiga.
 Zaune ta hango wani mutumi da alama security ne shi sabo da uniform dake jikinsa.

"Sannu malan"tace dashi.

" yawwa sannu"

"Dan Allah ina tambayar wata mata da kuma budurwa hannun budurwar rike da yaro mun taho tare suka bace mun"

Tsayawa yayi sannan ya danyi tunani kafin ya kara kallanta "nan corridor suka shiga zakiga daki suna daya daga cikin su"

"Nagode" tace jikinta har bari yake ta shiga,
Dakin na biyu ta tura kofar ahankali tare da lekawa,babu kowa acikin dakin sai mutun kwance akan gadan.
   Shiga tayi tare da tura kofar dakin,har bakin gadan ta karaso ahankali tana sanda.
   Har wajan gadan da Sapna ke kwance tana baccin ta cikin kwanciyar hankali.

Idanu ta zaro tare da rufe baki tana kallanta tana matsowa wajan nata.

Karan tafiya taji kamar za'a bude kofar,da sauri ta shige toilet din tare da karoshi ahankali tana kallan me shigowar tana faman nishi.

Shaheeda, mamah da kuma Aunty Rahma ne suka shigo dan Rahma taga Sapna.

Har wajan gadan suka tsaya sannan mama ta shafa ma Sapna kanta ahankali.

Bude idanta tayi tare da kallansu tana Murmushi, cikin sanyin murna Ta furta "mamah"

"Naam Sapna sannu kinji Allah ya kara miki lafiya ya saukeki lafiya kinji"

Safiya deke cikin toilet mamaki ya hanata koda kwakkwaran numfashi "kenan Sapna matar Fahad,ce itace kishiyar Salma, itace tasa akashe da hannun tah tabdi Jan"

Aunty Rahma ce ta kuma kallan Sapnar tare da fadin "sannu Sapna Allah ya kara sauki"

Murmushi tayi mata sannan tace "Ameen Aunty kema kinzo dama?"

"Eh ban jima da zuwa bah"

"Ya Sapna Anty Rahma fah ta haihu harda Bbynta tazo sunan baba gareshi amma Daddy ake kiransa" Shaheeda ta fada.

Kallanta Sapna tayi,
Gyada mata kai Rahma tayi alamun hakane.

"Ina yake Shaheeda daukomin shi inganshi"

"Toh" ta fada tare da fita dan ta dauko shi.
   Bata jima ba ta dawo dashi a hannun tah,

Kallansa Sapna tayi tana Murmushi "Allah ya rayashi Anty"

"Ameen Sapna kema Allah saukeki lafiya"

Rufe idanta tayi dan tana dan jin kunya,cikin ranta ta furta ameen,haka suma su mama suka furta.

Sannan suka juya zasu fitah.

"Mamah ki kawan abinci inci inajin yinwa"
Sapna ta fada.

"Toh bara a dama miki" sannan suka fita.

Ita kuwa Safiya na cikin toilet duk abunda ake akan idantah.

Bayan sun fita Sapna ta gyara kwanciyarta tare da rufe idanta dan ta dansamu sauki jin cikinta na yatsuna.

Ganin hakane yasa Safiya cire takalmanta ta rike a hannu sannan ta lallaba ahankali tana sanda harta fita ta tura kofar sannan tayi maza ta biyo hanyar corridor ta maida takalmin ta fita da sauri.

Bude idanta Sapna tayi jinkamar karan mutun,Amma bata ga kowa bah,hakanne yasa ta juya.


Tana fitowa gaba daya hankalinta ya gama tashi musamman da taga Maman su Sapna.
   Hannu ta zira cikin jakarta ta dauko wayarta hannun ta sai karkarwa yake.
   Kujera ta samu ta zauna dan ta sami nutsuwa.
   Number Umma tayi dailing, bata jima bah umman ta daga tare da fadin "wai lafiya ki kuwa Safiya?"

"Umma ina fa lafiya wlh Sapna na gani,da Shaheeda kai harda mamansu mah kuma qlau da itah,cikinema da Sapnar dan aurema gareta mijin kawata take aure Umma"

Wata uwar ashariya Umma ta dirka kafin ta kuma cewa "karyane Safiya karya kike tayama hakan zata yiyu"

"Umma Wallahi ba karya nakebah,nagansu gani gasu har magana kuma naji sunyi,dan Anty Rahma mah nan ta taho duba Sapna bata da lafiya"

Kashe wayar Umma tayi dan hankalinta yayi mugun tashi.

*★★*
Maza tayi ta shirya ta nufi wajan bokantah,dan ya yaudareta yace matah "bazasu taba dawowa daidaibah"

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Yana kwance yayi tatul da giya,yaji an bude kofar,ahankali ya daga idansa ya kallesu.

Manya manyan mazane guda uku suka shigo cikin dakin saikuma wani kamar dan China da lap cort ajikinsa,danne Kamal sukayi sannan wannan dan China yayi masa wata iriyar allura.
  A take anan yanayinsa ya fara canzawa idansa ya juye sannan ya fadi sumanme.
   Daukarshi sukayi har waje cikin motah.

Basu tsaya ko inaba sai Airport dan tafiya dashi China.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Lokacin da Umma ta isa wajan bokan tsayawa tayi tana mamakin yanda gurin ya koma,haka taci gaba da lulukawa canciki harta iske rumfar tashi.

Tana zuwa ta fara gaya masa korafinta

"Dariya yayi sannan yace da itah " hakane kuma muna sane,za'a miki aiki nahar abada Amma saikin kawo jariri sabuwar haihuwa tukun"

Shiru tayi dan tana tunanin ina zata samo jariri yanzu kuma sabuwar haihuwa.

Daga baya kuwa ta sanar dashi cewar ta amince kuwa.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Safiya kuwa kasa tashi tayi daga inda take zaune tayi.

*★★*
Bayan Salma ta fito daga wajan Likita ta zauna zaman jiran Safiya amma bata ganta bah,haka tayita nemanta,sannan ta koma wajan ajje motoci nan mah batanan amma motarta na nan.
   Haka tayita zaman jira amma shiru.

Mamace ta kirata ta sanar da ita Abbansu yana nan yana jiranta taje tayi zamanta,ga yinwa da kishi da takeji.

Mikewa tayi ta nufi bakin titi dan tare Napep ta tafi gida dan hankalinta yayi mugun tashi sabo da tana tsoran Abban su.

Tana tsaye bakin titi,
Wata hadaddiyar mota tayi parking a gabanta ahankali ya sauke glass din tare da lekowa yayi mata magana.

Ganin mijin Safiya ne wato Bash atunanintah,yasa ta kalle shi harta kuma gaida shi.

"Shigo mana na kaiki gidan mana"

"Aa Wallahi Nagode"

Murmushi yayi sannan yace "Nikuma yau Saina kaiki gida ko kuma muyita zama anan"

Budewa tayi ta shiga sannan ta kullo,"naji ka kaini Amma bahar kofar gida bah,abakin hanya zaka ajjeni saina karasa "

"Toh muje dai" ya fada tare da Jan motar sukabar wajan.

Suna barin wajan itama Safiya ta huce dan tama manta da batun wata Salma da suka zo tare.

*★★*
Suna isowa bakin inda zai ajjetah ta sauka shikuma yayi parking, hannu ya zira ya dauko mata kudi basu yawa yace gashi.

Amma taki amsa.

Lock din motar yayi yanda bazata iya fitah bah "kinga suma in kinki amsa samu zauna anan"

Suma saida ta amsa sannan ya barta ta fito bayan tayimai godiya.

Tana fitowa ta rufemai murfin motar sannan yaja ya tafi,dago kanta tayi tana Murmushi cak ta tsaya idanta ya fito,hankalinta atashe jikinta ya fara bari,ganin Abba cikin mota yana kallanta,Jan motarsa yayi yabar wajan da alama fita zaiyi...

"Innalillahi yau nashiga uku" abunda ta furta kenan.

Da er take daga kafafunta dan sun mata nauyi..






😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer😘*
[24/3 23:31] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳        ⚜      🌳🌳
🌳                              🌳
                👑👑
                   🌳
       *MARAICHI*❣
               *NA*
 *Zainab Naseer Sarki*
     *(Zeenaseer😘)*





8⃣8⃣


*Dedication to my fans Lov u much.........muah💋*




⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
*••••••••••*Haka ta taka har cikin gidan.
   Da sallama ta tura kofar dakin jikinta a sanyaye ta shiga cikin falon.

Babu kowa aciki,haka ta zauna saman kujera dan a tsorace take duk da tasan Abban baya gidan.

Mama ce ta fito daga cikin Kitchen tare da karasowa inda take kan kujera da dafa kafaduntah,"Salma kin dawo"

"Eh mamah na dawo Abba baya nan"

"Eh yanzu ya fita cikin gari"

Hannunta tazura cikin jaka tare da fito da wani dan karamin kati,
"Gashi enya dawo ki bashi na gaji zan dan kwantah"

"Amsa tayi tare da fadin toh,Allah ya kara sauki"

Batare data amsa bah tayi hanyar dakin su tana faman tafiya kamar kazar da kwai ya fashema ga ciki.

Binta Maman tayi da kallo tare da girgiza kai dan ita tausaya mata take gani take rabuwarta da Fahad ne ya sanya mata cuta.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Bayan mama ta dama ma Sapna custard sannan ta shigo har cikin dakin,ta tasheta zaune tare da jinginata jikin pillow sannan ta shiga bata ahankali tana dan mata hira harta sha da yawa.
   Bayan ta gama sha ta gyara mata baki tace da itah "mama inasan nayi sallah"

"Toh Sapna bari a kira Dr.ko zaki iya tashi kishiga toilet kiyi tsarki sana miki alwalar ki zauna ga kujera kiyi sallah"

Kai ta gyada mata sannan ta fita daga dakin.

Bayan 5mins da fitarta ta dawo tare da fadin "tashi Toh na kaiki."

Ahankali ta tasheta zaune sannan ta kamata ta kaita har toilet din,pant din jikinta ta cire mata sannan ta zaunarta kan Masan tayi fitsari tayi tsarki sannan ta maida mata.
  Alwala tayi mata sannan ta kamota ta zaunar da kujerar data ajje ta kalli gabas.
   Hijab ta saka mata sannan tace " yi sallar bara naje na dawo"

"Toh" kawai tace da ita sannan ta tada sallar"



Bata jimabah sosai ta kuma dawo wa,zaune ta ganta kan kujerar ta idar da sallar tana addu'a.

"Toh kin idar sannan bara na maida ke kan gadan ko kyafi jin ddi"

"Aa mama dan Allah ki kaini dakin da kuke nan ni kadai ake bari bana jin ddi"

Murmushi tayi sannan tace "Aidan kar a dameki da hayaniya shiyasa"

"Aa nide muje can din"

"Toh mike muje" sannan ta kamata ahankali suka fito daga cikin dakin har zuwa wancan dakin.


Hajiya ce tace "aa jiki ya fara sauki har an fara yawo"

Dariya ta danyi dan ba karamin dadi takeji bah inta bude Ido taga en uwanta bah.

Kusa da Mum aka kwantar da ita sannan ta Dora kanta bisa cin yar Mum din.

Auntyummie ce tace "yo ni ai bama ajin kunyar surukai an dane cinyar" ta fada cikin zolaya.

Dariya duk sukayi "Sapna ai er gata ce,intana gaban Mum tana nanike da ita en kika haihu ai abarma bbyn ciyar ko?" Aisha ta fada.

Mum ce tace "toh Aisha kinfara tsokanar tatah ko daga farfadowartah"

Dariya Hajiya tayi sannan tace "Rabu da itah ita da mijin tah"

Hhhhhhhh"Haba Hajiya aiba abunda zaimun"

"Toh kick gaba da takurawa matarsa kigani in ba'a kura kuba"

Dariya sukayi gaba daya.
  Itade Sapna saide ta kalli wancan ta kalli wancan bata magana sai faman Murmushi take.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Fahad ya sanya An gyara gidan Sapna kamar babu abunda ya faru.

Haka Dad yasanya ayita bin cike harsai an gano wanda ya aikata wannan Abu,har lokacin babu wanda yasan Fahad ya saki Salma.

Haka babu wanda ya damu da rashin zuwanta asibitin dan ansan dama ba san mutane take bah.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Tunda Safiya ta koma gida ta rasa abunda yake Mata dadi gaba daya hankalinta da zuciyarta sun shiga cikin rudani,ta kasa zaune ta kasa tsaye.

Tabbas ta tafka babban kuskure,inhar ta bari aka kamata da wani idan zata kalli jama'a ta sanya anyima er uwarta irin wannan cin mutunci.

Daga wancan kujeran zuwa wancan kwata kwata ta kasa sukuni.

Gashi tun dazu take kiran Umma amma tamaki daga kiran nata.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
*5:15pm* daidai wannan lokacin jirgin su Fahad ya tashi zuwa China har lokacin baya motsi tamakr matacce haka ya koma.

Haka can kasar China Leon yana can yana jiransa dan cimai mutunci saboda ya cimasa kudi masu din bin yawa bayan yaudarar sa da yayi.

*★★*
Shikuwa Bash tunda ya kyallah idansa akan Salma ya kudiri niyar itama saiya yaudareta kamar yanda yake shirin yaudarar Safiya.

Shiyasa zai damari niyar koma menene zaiyi dan cikar burinsa.






😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer😘*
[24/3 23:32] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳            ⚜            🌳🌳
🌳                                        🌳
                    👑👑
                       🌳
            *MARAICHI*❣
                   *NA*
       *Zainab Naseer sarki*
           *(Zeenaseer😘)*





8⃣9⃣




*Pls kuyi hakuri na rashin yin post akan lokaci pls Nagode da kulawarku💋*




⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
*•••••••••••••*Salma tunda ta dawo gida hankalinta ya ki kwanciya dan jiran Abba kawai take yazo dan tasan ta shiga uku.

Bayan ta idar da sallar magriba tana kwance kan gado kamar bacci take amma idanta biyu.

Da sallama mama ta turo kofar tare da shigowa.

"Salma" mama ta kirayi sunan tah.

Bata amsa mata bah illa dago kanta da tayi tana kallantah.

"Abbanku ke kiranki "

Gabantane yayi mugun faduwa sabo da kiran da taji Abba yayi matah.

"Toh"ta fada tare da mikewa ta saka hijab dinta sannan ta biyu bayanta.

da sallama suka shiga ciki falon.

Yana zaune kan kujera yana kallan *Aljazira* daga dan nesa dashi kadan ta durkusa.

Ahankali ta furta "Abba barka da dawo wah"

"ywwa ya jikin naki"ya amsa matah,

"Alhmdullh" itama ta bashi amsar kanta akasa.

bayan shiru na en mins sannan ya kuma cewa "Salamatu duk abunda zakiyi ki kasance kin kiyaye mutunci ki,ke babbace basai angaya miki ga dai dai bah,iri su Zulaihat su za'a ma fada ba kebah,Amma ke kullum cikin fatama mutane rai kike"
yana magana yana kallantah.

Mamah kuwa shiru tayi dan bata masan meya handasa fadan fah.

"Yanzu shi wannan aina kika sanshi?"
ya jefo mata wannan tambaya.

bakintane yayi mata nauyi,da ker ta iya dagashi tare da fadin "Abbokin Fahad ne yaganni bakin hanya ban samu Napep ba shine ya taimaka ya rageman hanya"
Ta fadi hakanne da kar yayi tunanin wani abun.

Kallanta kawai yake da idansa,amma ko kadan be gamsu da abunda ta fada masa bah.

"nide nagaya miki ki kiyaye tam,tashi ki tafi  Allah ya kara sauki"

ko Ameen din bata fada bah,ta mike ta nufi dakinsu dan arayuwarta bata kaunar fada dan ita gani take yanda Abban ya takura mata anyama shine Babantah.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Yau en asibiti da huri suka tafi dan da baki,Hajiya da Shaheeda yauma aka bari.

suna zaune cikin dakin nasu,wanda har lokacin Sapna nanan akwance,dan tafisan nan dakin,koda za'a mata allura anan aka matah.

da sallama Annur ya shigo cikin dakin tare da zama kan kujera.

bayan sun gaisa da su Hajiya yace "Yame jikin"yana kallan Sapna dake kwance jikin Hajiya ita din shi take kallo tana Murmushinta me rikitashi.

"Jiki kam Alhmdullh am fara samun sauki kanaga anki zaman can dakin"

Murmushin shima yayi sannan yace "Gaskiya ai dole tafi san zamannan din dan tafi ganin jama'a tunda can shiru ba kowa"

Kallanta yaci gaba dayi,dan so yake ya rungumetah ko yaji dadi,gashi kunyar Hajiya yake ji dan en Shaheeda ce kadai bama komai.

Dabarace ta fado mai,yace da itah "toh tunda dare yayi gashi kuma Kin fara jin bacci tashi amaidake can din,kar kisa Tsohowa wahala"

Dariya hajiyar tayi tare da fadin "Yo duka nawa take da zata sani wahala saide dan girman cikin natah"

Itama dariyar tahi,dan tanasan taje wajan Fahad din ntah.
ahankali ta fara mikewa zaune.

da sauri ya mike tare da dukarta cak!

saida safe tama su Hajiya sannan suka fita daga dakin.

kan kadan ya sauketa Hankali sannan ya gyara mata kwanciyar.

zai kuma ya zauna ta ruko Hannunsa tare da fadin "Ina ka tafi tun dazu kaki dawo wa"ta fada cikin Muryar shagwaba.

Murmushi yayi tare da mata kiss a bakinta "am srry Soulmate baki nayi daga lagos danni banma san da zuwansu bah saida  Abba ya fada,akan saban Company n mu nacanne za'ayi magana"yana Magana yasna shafa mata fuskart.

Murmushi tayi masa tare da fadin "Allah ya bada sa'a Hubbyna"

"Ameen i lov u"

"I lov u too Hubby"

kansa ya hada da nata yana kallan idantah.

ahankali ta furta "Hubby kowa yazo dubani amma meyasa Anty Salma bata zo bah"

"don't wrry bbyna,Bazata zo bah"

"toh amma meyasa kona mata laifine"

"No baki mata komai bah,just abar maganarta kinji "

kai ta gyda masa tare kissing hannunsa dake gefan chick dintah.

"bakya bokar wani abun?"
y tambaya yana shafa cikintah.

lumshe idanta tayi tare da fdin "Babu komai naci abinci na koshi kuma gaka agabana,ina ganin shine abund nafi bukata koma nasamu"

Rigarta ya yaye ya shiga kallan cikin nata duk an nannadeshi da bandage.
kiss kasan cibiyara yayi sannn ya gyara mata rigr.

matsowa yyi kusa da fuskarta tare da saka ahannunta yana shafa mata lips dinta "Soulmate in kika Haifa mana yara twins Hani suna za'a saka musu?"

Murmushi tayiidanta a lumshe sannan tace "in maza ne sunan Dad da Babanmu in kuma Matane Sunan mamah da Mummy"

"wow! Allah ya saukeki lafiya kinji"

"Ameen Hubby"

Ahankali yaringa shafa mata kanta yana hura mata iska cikin kunan tah,nan da nan Bcci ya dauketah.

saida yayi mata addu'a ya shafeta da ita sannan ya mata gudnyt kiss sannan ya fita tare da kulle kofar.

Su Hajiya yayima sallama sannan ya tafi gida.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Lokacin da suka isa Kamal be farkaba dan Haka kai tsaya wajan Leon suka kaishi,bayan ya biyasu kudinsa,yasa aka kaishi can cikin wani gida yace a ajje masa shi harsai lokacin daya damar afitodashi.
       Haka kuwa suka dukeshi suka kaishi.


♣♣

Safiya itama har lokacin taki dawowa daidai.
    tana kwance saman gadantah tayi rufda ciki tana wasa da wayarta dake gefanta abun duniya ya ishetah.

wayar tace ta kama ringing kamar bazata daga bah kuma saita daga.
   jin muryar Umma ya sanyatah tashi zaune.

Umma ce tace da itah "Safiya ki kwantar da hankalinki dan wadan nan jarababbun mutanan munkusa rabuwa dasu har abada"

"Haba Umma gaskiya ki kyalesu haka,bafa abunda suka tsare mana gaskiya ni yanzu mah abunda namusu nake nadama"


"Nadama? Nadama fah kikace Safiya lafiyarki qlau kuwa?"

"Ni lafiya qlau nake,ni Allah ya ganar dani,zanje nasamu er Uwata na nemi gafarar ta kuma kema yakamata kizo ki nemi gafarar Su tunkafin ki koma ga Allah dan Allah Umma"

tsaki tayi sannan ta kashe wayar.

tsayawa tayi da wayar ahannuntah nan danan kuka ya kwace matah,kuka tayitayi tana rokwan Allah ya yafematah.








😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻 🌷







*Written by  Zeenaseer 😘*
[24/3 23:32] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳              ⚜          🌳🌳
🌳                                        🌳
                     👑👑
                        🌳
            *MARAICHI*❣
                     *NA*
      *Zainab Naseer Sarki*
         *(Zeenaseer 😘)*





9⃣0⃣





*••••••••••*Bayan sun Gama waya da Safiya fada tarinka yi Dan Safiya ta fata mata rai sosai.
  Kuma ta kudiri niyar abinda taga dama babu Wanda ya isa ya hanata.


*BAYAN WASU WATAN*

Zaune Sapna take acikin falon mum cikinta ya tsufah tayi kiba takuma Kara kyau kamar ba itaba sai faman cikin kwadan xogale take.

Gefanta kuwa Shaheeda ce zaune Tana chat lokaci lokaci takan zuro hannu tadan dauki zogalan.


Tun Bayan da aka sallamu Sapna daga asibiti ta dage ita zata tafi da ita gidanta haka Mamah ta Hakuna badan tasobah ta barta ta koma candin harta haihu sannan ta koma gidanta.
    Ta Samu lafiya sosai Dan Tana samun kulawa wajan Mum.
 Haka kullum fahad zaizo inzai fita da Kuma inya dawo.
  Ranar weekend Kuma yini yake agidan,yana nunawa matarsa soyayyah da Kuma babynsu.
   Duk abinda,ya kamata asiyama bby da Kuma mamansa, sun Gama siya,zuwan sa kawai ake jiran.

♠♠
Ban garan umma kuwa har yanzu bata Hakura bah, jira kawai take lokacin da bokanta ya bata da zaa Fara aiki yayi.


♣♣
Salma kuwa har yanzu Fahad yaba batun maidata gidanta,haka Kuma Abba ya Hana aje gidansu Fahad ayi magana.
   Har lokacin ba'a san wadanda suka aikata laifi nanbah.

yanzu sun jone da Bash, sosai yake kashe mata kudi,amma agida saita ce kudintane taja jari dashi haka aka samata ido tanata faman business dinta yawo ba dare ba Rana.
   amma bata taba yarda wani Abu ya hadata da shiba, lokacin datasan Bash ba mijin Safiya bane tayi mamaki sosai Tun daga lokacin ta Fara kishi da ita hakan ya janyo basu tare yanzu Kuma ta dauki niyar raba Safiya da Bash dinner kuta yayane.


♣♣
Har lokacin itama Safiya ta kasa zuwa wajan su Sapna Dan Tana ta tsoran yanda zata dauketa amma tadau alkawarin Sapna ta haihu zataje ta gantah.


Duk Wanda Umma ta raba da su Sapna sun dawo garesu yanzu suna jin dadi Dan en uwa kuwa ji yake dasu, haka Dan Asabe da matarsa har gida sukaje gurin Mamah sannan suka duba Sapna.
    Haka itama Hafsa tace inde Sapna ta haihu zataje Dan ta yafe mata itama abunda tayi mata.
 

Kamal kuwa yana wannan gida babu abunda ya rasa cida da sha da Kuma sutura amma babu inda yake fita sai de yana wannan gidan.
    cikin Wanda ke tsaransa ya Samu wani amini Wanda Duk ya fadamasa sirrin dukiyarsa Kuma yayi masa alkawarin tabbas zai bashi ita amma harsai ya kawo masa Sapna da zuciyarsa ta haukace bisa San da yake matah.
   Haka kuwa shima ya baza yara anan Nigeria har saida aka gano Sapna Kuma suna nan suna fakon saceta mundin suka Samu damar yin hakan.
    sannan ya sanya a kashe Mai bash Wanda shima Bash din yana sane da hakan Dan kawai Wanda ke cikin su Kuma abokin Bash dinne shiyasa yake kamfa kamfah.


♣♣

Bayan La'asr Shaheeda ta dauki Jakarta tare da gyara fuskarta, Sapna na zaune Tana kallanta Dan tasan zata iya cewa tafiya zatayi.

 Saida ta Gama shirinta sannan ta Kalli Sapna tare d fadin "Ya Sapna tafiya fah zanyi "

"Kai Shaheeda bazaki kwanaba Dan Allah ki bari sai gobe sainama Mama waya"

"Gaskiya nide ya tafiya zanyi kullum ke akazo zai kice mutun bazai tafi bah"
Murmushi tayi tare da fadin "Haba er kanwata Dan Allah ki bari sai goban mana"

Da sallama Mum ta shigo cikin gidan da alama daga kasuwa take.
   zama tayi kan kujera tare da fadin "washhh Allah Nagode mah"

sannu da zuwa suka mata sannan Shaheeda ta kawo mata ruwa.

"Shaheeda bara na Kira Mama kinji Dan Allah "

banza tayi da ita tare da daukar Jakarta.

mum ce tace "awe!  Yau baza'a kwanan manan bah"

Sapna ce tace "Nima rokwanta make to wallayi Duk yanda akayi ya saif Ne zai zo Yau *(Dan gidan Yaya Babban yayan su Maryam shike San Safiya)*

harararta tayi tare da fadin  "Toh ina ruwanki inma shine zaizo din "

Dariya Mum tayi tare da fadin "Aa babu ruwanta ayi hakuri amma kin yarda gobe zakidawo kiyi mana weekend anan? "

Kai ta Gyada tana Murmushi.

"Toh maza kice da Ado driver ya kaiki"

sannan tayi musu sallama ta tafi.


♣♣
Umma kuwa bokanta yayi kiranta ya sanar mata data samo jariri daran Yau Za'a Fara mata aikintah.

cikin farin ciki ta shirya ta nufi asibiti Dan sunyi da wata Nurse ta biyata makodan kudi da zata sama mata yaro saban haihu Duk Ranar da tasobah.

Tun Tana cikin motar sukayi waya da ita takuwa mata da albaishir yanzu aka kawo wata mata Tana labor.

nan kuwa Umma ta Kara Sauri.

Bayan kamar 30mins da zuwanta asibiti Nurse ta sanar mata data zauna cikin motah zata kawo mata yaro.

Umma na zaune cikin motah misalin *11:51pm* ta hango nurse rike da yaro tanata sauri da kaganta kasan bata da Gaskiya.

yaro kuwa Ashe tunda yazo duniya bashi da rai haka ta ha enceta ta kawo mata shi.

lokacin data iso wajan motar Tana isa ta Mika mata sannan tayi godiya takuwa Kara mata WASU kudin.

Duk kuwa abunda ake wani mutumi na zaune yana kallansu.

hakan yasa ya dauki machine dinsa yabi bayantah.

ita kuwa Umma ana kawo mata yaro wajan bokanta yatanufi dashi Dan Duk tunanintah bacciyake.


Duk inda ta shiga wannan mutumin na biye da ita harta isa inda tayi parking ta fito hannu rike da jariri ta shiga bin hanyar ko tsoran dare bamatayi


shima binta yayi yana labewa.

Tana isa dama boka yace ta ajje yaran cikin wata korya haka kuwa taga korya takuwa saka yaro acik sannan ta shiga motah ta barwajan.

Duk abunda ake akan idan wannan mutumi.

Tana barin wajan yabi Bayan tag.

har saida taga gidantah sannan ya juya ya Koma asibitin.

lokacin daya isa Dan ganin matarsa daya Kai me tsowon ciki kota haihu Dan Kuma taya tona asirin wannan nurse Dan yaganetah.

yana isa aikuwa ta hangoshi ta karaso gareshi tare da fadin "kaine ka kawo matarka zata haihu "


"kwarai kuwa nine"cikin mutanan dake zaune wajan ya bata amsa.

"saide kayi hakuri Allah yayima bbyn rasuwa saboda cikin be isa haihuwa ba Dan bbynma ba complt bane saide kayi haK......... "

bata gama maganar bah ya dauketa da Mari ya Kara mata nan ya hauta da dauka kamar Allah ya aikoshi,


mutanan dake wajan sukaji abunda suke fadane suka taso da sauri aka kwacetah a hannun sa.








😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer 😘*
[24/3 23:32] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳             ⚜           🌳🌳
🌳                                        🌳
                     👑👑
                        🌳
            *MARAICHI*❣
                     *NA*
     *Zainab Naseer Sarki*
        *(Zeenaseer 😘)*






9⃣1⃣





*••••••••••••*Wani daga cikin mutanan Ne ya jashi gefe tare da fadin "Haba bawan Allah, in kowa haka yake Aida ba'a jima bah, daga ta Gayama sakon mutuwa saika hauta da duka "

"kallanshi ya tsaya yi sannan yace dashi "wannan matar munafukace, ina ta kaimun Dana, ku sakeni wallayi saina tona mata asiri "yana magana yana nunata

Yayin da ita Kuma sai faman muzurai take alamun rashin Gaskiya bakinta na zubar da jini.

Mutumin Ne ya Kara fadin tare da Kuma nuna tag "Wannan matar munafukace wallayi yaran jama'a take saidawa,inkuma karya nake ta musa"

kanta a kasa gaba daya rashin Gaskiya ya bayyana GA fuskarta.

mutanan dake wajan duk mamaki ya kamasu wasu kuwa sai Allah wadai suke,

"malam kana da Gaskiya wallayi kokiyi magana ko mu konaki wajan nan"
Wani Mutumi ya fada.

kuka ta Kama Tana rukonsu da su rufah mata asiri asiri zata fada.

wata nurse na ganin abunda ke faruwa tayi maza ta Kira me asibitin, nan danan kuwa yazo hankalinsa atashe.

yana karasowa ya Fara rukonsu dasu kwantar da hankalinsu akaita GA ensanda Dan shima bazata batamai sunan asibitin Sarah.

haka kuwa suka jata zuwa, police station.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Umma kuwa tunda ta koma gida ta kasa bacci da tsabar farin ciki, saboda bukatarta zata biya.
    Haka tayita farin ciki ta rasama Wanda zata fadama suyi murna tare Dan tunda sukai magana kwanaki da Safiya ta dena kiranta kota kirata bata dagawa.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
Bayan Shaheeda ta tafi gida, Sapna daga ita sai Mum sun Gama cin abinci tana dakinta zaune kan gado Tana duba hani littafi na babies.

Fahad Ne ya turo kofar dakin da sallama tare da zama kusa da ita.

"Mumtwince Yau lefin me nayi ba'a kirani bah"ya karashe maganar yana kallanta.

Murmushi tayi sannan tace "Yau yarankane suka dameni da motsi shiyasa Dan bana jin dadin jikina sosai wallayi "

"Ayyah "ya fada tare da matsowa jikina ya dora kanshi saman cikin Nata, "Soulmate ko labor en Ne yazo muje asibiti.

"Haba de ai Mum tace ba haihuwa bane, hakan de suke kicking maybe dey need deyr Bappa near dem"
Itama ta fada Tana shafa masa Kai.

zaune ya Mike tare da kallan tah"Soulmate Mum bata sona ta hanani na sake da matatah, pls kice mata kinasan komawa gidanki"

"Hubby kaima kasan it's can't be possible Kama dena fadan haka "

"But Soulmate I also........ "

bakinta ta hada da nasa bema karasa maganar bah, tsawon Lokaci ahaka harta Kai ga kwanciya aka Fara knocking kofa.

da sauri ta tureshi tare da gyara rigarta Dan tasan Mum ce, shikuwa Duk ya rikice idansa harsun canza Kala zuwa red.

Ahankali ta shigo dakin amma abakin kofa ta tsaya.

har lokacin Yana faman kallan tah da runannun idanunsa.

"Fahad kazo Ka huce zamu kulle gidan"

shiru yayi kamar zaiyi kuka, Dan baiji dadi bah, kamar yace anan zai kwana, sai Kuma Yamike tare da kissing neck dinta sannan yace "gudnyt"batare daya Kara magana bah yafice daga dakin.

Mum de girgiza kanta tayi dan rashin kunyar Fahad ta ishetah sannan ta Kalli Sapna da kanta yake a sunkuye tace da ita "Baki Bukatar komai Sapna? "

"babu Mum"ta fada batare data Kalle tabah.

"Toh sai Allah ya kaimu"sannan taja mata kofar.

Ahankali ta kwanta Ahankali Dan ciwon da bayantah ke matah.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Zaune Salma da Bash suke a kofar gidan su Salma cikin motar Bash din.
 
"yanzu babu yanda Za'a Abba ya barki Muyi tafiyar nan tare? "

"Bash kenan,wallahi nayi iya kokarina amma abun yakiyi saide katafi kawai saka dawo ai muna tare "

Shiru yayi yana kallanta sannan yace "Nan da 4dys Nakasan tafiya kafin na tafi kawai wasu kudi da zan baki sai mu hadu ko zuwa jibine insha Allah.

"ohk ba matsala zansan yanda Za'a ayi kaide na gode sosai "

Sannan ta fita ta shiga gida, sai faman binta yake da kallo harta shige gidan.
Murmushi ya Kuma yi sannan yaja yabar gidan.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑

Washe gari da safe misalin *8:25am* En sanda suka isa kofar gidan  late..Alh. Ibrahim Dan ganin Umma.

ko tashi daga bacci bah Tana kwance suka shigo gidan.

jin karar sallama ne ya Sanya tah tashi tare da fitowa waje.

karaf! Female police suka kamata tare da fadin "Ur under arrest ma'am"

umma ido ta Fara zarawa tare da fadin "Lafiya Kuma bayin Allah me Kuma nayi?"

Babban cikinsu Ne ya kalletah tare da fadin "In munje can kyaji koma menene?

"Dan Allah kuyi hakuri Ku taimaka "ta fada Tana kuka "Toh ku bari nakira Dana Dan Allah "

Duk majiyar da take haka suka tasa keyarta har cikin motar suka tafi da ita.


wannan mutumi na tare dasu shinema ya kawosu gidan.
   Kai tsaye wajan boka suka nufah.
    lokacinne hankalin Umma ya dada tashi Dan bata taba tunanin kawai Wanda ya kamata bah.

koda suka isa wajan bokan, basu tarar da kwaryar da mutumin ya fada ya gani bah.

haka suka shiga wajan har Umma suna turata.

boka na zaune cikin bukkar sa yaga Umma tare da en sanda.

Dariya ya kamayi kafin yace "ke shine kika kawomin hukuma har cikin gdana"ya daka mata tsayatsawa,girgiza kanta ta shigayi alamun Aa,

'"Toh lallai kinyi Babban kuskure tabbas zaki hadu da fishi na da Kuma hukunci me tsanani"

yana kaiwa nan ya bace bat!  nan suka shiga nemansa amma basu gansaba, haka sukajah Umma har cikin mota sannan suka bar wajan dan zuwa police station, shikuwa mutumin kuka ya kama saboda rashi sanda.



Kai tsaye can suka nufah.






😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB* 💅🏻 🌷





*Written by Zeenaseer 😘*
[24/3 23:32] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳             ⚜           🌳🌳
🌳                                        🌳
                     👑👑
                        🌳
           *MARAICHI*❣
                    *NA*
    *zainab Naseer Sarki*
         *(Zeenaseer 😘)*




9⃣2⃣





*••••••••••••*Suna isa kafin su shiga ciki Umma ta Fara Dariya Tana yaga gayanta, haka yasa suka daure hannunta suka shiga da ita ciki.
   Nurse na zaune Tana ganin umma haka, mamaki ya kamata.

Suma en sandan mamaki suka kama, nan suka koma Dan kiran wani Nata, koda suka isa basu tarda Dan bata bah, sai Rahma ita Kuma ta Kira Dan asabe ta Kira, shikuwa yace bama ya gari Kuma Koma yana nan babu abunda zai matah.

Haka kuwa Rahma ta sanar dasu, suka koma kuwa suka dauko ta suka maidotah gidan, Dan sun San aikin boka Ne.
   Ita Kuma Nurse suka yanke mata hukuncin 20yrs a prison.

Bayan sun maido Umma gida haka taci gaba Da surutantah, Tana yaga kayan jikin har saida tayi tsurarah, haka Rahma ta sakata cikin daki ta kulle ta, haka taci gaba Da bari cikin dakin.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
Tunda Sapna ta kwanta daran Jiya haka tayita juyi amma ta kasa bacci, Tun tana jin ciwon kadan kadan Harde ta Mike zaune.
      Falo ta fito ta nufi, fridge ta dauko ruwa Tasha sannan ta maidah.
   Zama tayi saman kujera Tana faman ya tsuna fuska kamar zata yi kuka.
    sai Kuma ta tashi, tarinka, Hawa upstairs Tana saukowa,tun Tana abun kamar wasa, saita tashi ta koma dakinta, haka Kuma ta koma zaryar fitsari.

har aka Kira sallah asbah amma Tana Abu daya.

saida Mum ta fito da yake Tana zuwa dubata da asbah.

ganinta a hargitse Mum ta San ba lafiya.

"sannu Sapna bara mu tafi asibitin koh"

ko kallanta batayi bah taci gaba Dayawantah.
Haka ta Mike ta dauko hijab dintah, tadukowa Sapna Nata amma fir taki yarda ta saka.
    bata magana dama duguwar rigar material ce ajikintah,kanta ko dankwali babu Gashinan ya zaba bayantah wani ya manne fuskarta da huyantah sabo da gumin da take hadawa.

daker ta shiga motar suka tafi asibitin.

koda sukaje asibitin aka ce haihuwa ce amma da saura ba lokacin bane.

Mum wayarta ta dauka ta Kira Mama. Nan da nan tashirya Dan tafiya Dan Hajiay bata nan sun tafi Umarah, sai ita da Shaheeda suka tafi asibitin.
   Shaheeda ce Takira Fahad nan nan ya rikice, ya taho asibitin.

koda su Mama suka isa, haka suka tarda Sapna Nata safa da marwa tana sallati, inta gaji ta zauna, sai faman sannu suke matah.

haka shima Fahad daya iso haka ya tarda tah.


har kusa *10:04am* Sapna bata haihuwa bah.
gaba daya jikinta ya jigata,tama kasa yawan.

Dr. Shehu yace Gaskiya yaga ta wahala gashi har yanzu ciwon karuwa yake, yace da Fahad ko amatah *CS* amma Mamah tace abari tukun zuwa anjimah.

haka Sapna Tasha wahala kamar zata mutu Dan Fahad da Shaheeda kuka suka rinkayi sabo da tausayi.

misalin  *10:49am* Sapna ta haifi santaleliyar yarinyar tah, me kama da ita Tasha kuka da kiraye kirayan sunaye..

Fahad kasa hakura yayi, cikin dakin ya shiga ya ganta kwance jikinta ya Jigata ta jike sharkaf da gumi gashin kanta yayi lufluf ya kwanta.

rungume tah yayi yana kukan dadi yama Rasa ya zaiyi Dan murna.


wani saban ciwonne ya Kuma taso mata nan yata damke hannunsa Tana kiran sunan Allah.

"Sannu Soulmate Allah ya saukeki lafiya Sannu "

"Wayyo Fahad mutuwa zanyi, Wayyo shikenan mamatah,zan mutu"

"bazaki mutu bah, insha Allah sannu "

haka tayi tayi har kusan 30mins sannan wata bby girl din ta fito.

Hamdala Fahad yayi sannan ya dauketa be damu da jinin dake jikin taba, nan Ta Fara kuka.

Murmushi yayi Yatsaya yana kallanta, tabbas Yau ta kasance babbar Rana gareshi, Ashe dama zaiga jininsa, Yau gashi shi aka haifama en biyu abunda yafi so kenan wato bbygirls Yau gashi Sapna soulmate ta haifah masa.

matsawa yayi harda hawayansa ya mata peck a goshi tare da fadin  "tnkuuuu so much soulmate ur my everything I love you "

Nurse Ne suka amshi dayar sannan suka miko masa Wanda aka shirya ya amsheta tare da mata addu'a da Kuma mata hudubah da sunan Mama watoh  *Maryam* fita yayi daga dakin, bbyn na Hannunsa Dan zasu gyara Sapna.

Mum na hangoshi rike da Bby ta taso tare da amsarta itama harda kwallar a idantah.

addu'a itama ta mata tare da fadin  "Tubarkallah Masha Allah,Allah ya Raya mana " sannan ta Kalli Fahad dake Murmushi yana kallan bbyn yace sunan Mamah Ne?

Murmushi ta kumayi sannan tace  "Maryam" mikawa Mamah ita tayi sannan ta zauna kusa dasu.

itama Maman addu'a tayi mata ta nuna farin cikintah sosai sannan ta mikawa Shaheeda dake San daukarta Tun tuni.

"Wow!  Gaskiya tafi ya Sapna kyau kama da Ya Fahad Take" Kowa sai kallanta yake ita kuwa bacci taketa faman yi.

Dakin ya koma ya amso dayar ya fito musu da ita Bayan ya mata hudubah da sunan Mum *halimatussadiya* sannan ya kawo ta.

sosai suka kasa boye farin ciki sai murna suke Mum kamar zata hadiyesu Dan wani mugun sansu da takeji.


Haka Shaheeda tayi ta daukarsu a pics Tana dorawa a social network.


Bayan an Gama gyara Sapna aka kaitah dakin Hutu, sannan aka basu iznin ganintah.

dukkansu suka shiga dakin kowa yana murna.
sannu suka shiga mata kamar zasu cinyetah Dan so da Kuma kulawa.

"ya Sapna dama kince inkin haihu zan zaba wa yaran Nick names ko? "

Murmushi tayi tare da fadin "eh"

"ywwa me sunan Mamah itace *HANANSA* ita Kuma me sunan Mum  *HULUD* "

"toh kaji iyaye har an zabama yara suna "

Murmushi tayi sannan tace "Mamah dama ke kadai zaki koma Ni ina tare da Angels "

☺☺ Murmushi mama tayi sannan tace "Toh tawaye zaki min kenan "

haka akaita bar kwanci.
har Yamma tayi sannan aka sallamesu.


*♣♣*
Safiya ta Yima Sapna siyayyh me tarin ywwa Dan tace Tana haihu zata Je Dan ganin yarantah.

Haka takan Kira Sapna har suyi waya amma har lokacin saide tace mata wata class mate din tace ita Kuma harta yarda ta Kuma mata alkawarin inta haihuwa zata sanar matah..







😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL  FAN'S  CLUB*💅🏻🌷






*Written by Zeenaseer 😘*
[24/3 23:32] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳             ⚜           🌳🌳
🌳                                        🌳
                     👑👑
                        🌳
            *MARAICHI*❣
                     *NA*
      *Zainab Naseer Sarki*
         *(Zeenaseer 😘)*






9⃣3⃣





*••••••••••••*Bayan su Sapna sun dawo gida da twince.Nan da nan gida yafara cika da jama'a Duk da cewar dareni.
   Fahad an kasa zama sai hidima ake yana ta kiran abokansa yana sanar musu da haihuwar da aka masa.

Haka Mamah ce Tama Sapna Wanka, sannan ta gyara jikinta sai kanshi take. Bayan ta ci abinci sannan Mum tace ta kwanta ta huta.

Aikuwa Tana kwanciya nan danan bacci ya dauketa Dan dama tana Bukatar hutun.

Mum ce tayima twinz wanka ta shirya su cikin kaya white sunyi kyau kamar Kasace su Ka gudu,haka aka kwantar dasu cikin Dan karamin bed dinsu da Fahad ya siya musu Suma baccin sukayi.

Shaheeda kuwa tana kusa da yaran ko kadan batasan abunda zai tasheta daga wajansu.
    Motsi kadan tayi musu hoto Dan daga haihuwarsu zuwa yanzu ta musu hoto ba adadi.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Safiya zaune cikin falon ta Tana waya Bayan Tagama Ne takira Salma Dan sun jima basuyi waya bah.

Har ta yi ringing ta Gama amma ba'a daga bah, amma ta Kuma kiranta harta kusan katsewa ta dauka tare da fadin  "hello! "

Murmushi Safiya tayi kafin tace "Salma menene Kuma duniya shikenan an zama Manya ko neman mu ba'a yi"

"hmm Safiya Bahaka bane kisan Yanzu abubuwa sunyi Yawa bani da lokacinne amma inasan zuwa wajan naki"

"Toh Allah ya taimaka sai kin shigo din"

Sannan sukayi sallama ta kashe wayarta tare da sakin Murmushi.

Dan Adam kenan, yanzu duk yanda muke da Salma amma abun duniya ya rabamu da ita,allah ya kyauta.

har zata Kira Sapna sai Kuma tayi tunanin dare yayi kar tayi baccinta ta takura matah amma tayi alkawarin gobe da safe zata Kira tah.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
Washe gari da safe, Rahma ta tashi Dan duba umma ta Kira Abba Dan ta sanar masa amma har lokacin wayarshi akashe.

tausayintane ya kamata ta dauko abinci da Kuma ruwa ta nufi dakin Nata data kalletah Jiya.

Koda ta isa,ahankali ta leka amma bata gantaba kuma Bataji alamun motsin tabah.

Ahankali tane ya tashi Dan tunanintah ta mutu.

da sauri ta zubda abincin sannan ta bude dakin Dan dubata.

kwance ta ganta cikin kaya tayi kaca kaca da dakin dama kana shigowa zakaga da dakin mahaukata ya dace a Kira shi.

Duk ta jima jikinta ciwo, gata tsirara sai Wanda karamin ajikintah.

bata tasheta bah, illah dakin data kulle sannan ta shiga ta dauko duguwar Riga Tana ta bacci ta saka mata sannan ta shiga cire matah kwalbar data taka a kaFarta.

da sauri ta Mike zaune tare da kwashewa da Dariya sannan ta Mike ta Fara jijjiga kofar, aikuwa tayi sa'ar budetah.

da gudu ta fita Tana ihu, Rahma ce Tabiyota Tana fadin "Karki fita tsaya"

amma ina tini tayi waje Tana haukanta da Dariya.

binta yayi tana Kira tare da neman Taimako mutane.

wasune suka kamata Dan kaitah gidan mahaukata sannan Rahma ta dauko mota suka kaitah.

Bayan Tadawo gida da yake suna mutunci dasu Hafsa nan takira ta sanar musu da abunda ke faruwa.

kuka suka shigayi dan sun San abunda ta shuka take girbah.

sunce de zasuje su dubata ta Kuma zasu mata addu'a akan Allah ya yafe matah.


👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
Washe gari da safe Bayan Mum ta Gama shirya yara sannan ta Yima Sapna wanka.

Suna zaune misalin *11:00am* sun Gama breakfast mama ta iso itama Aisha tazo,kafin ajima gida Ya cika da jama'a Dan Mum Nada mutane.

kowa yana sha'awar yaran gasu kullum cikin kaya masu kyau suke.

Ana Falo anata hira ita kuwa Sapna tana daki tana hutawa.

Dan har Fahad yazo ya gansu ya huce office.

wayar tace tayi Kara daukota tayi tare da karawa GA kunnuwanta.

Bayan sun gaisa ta gaya mata class mate dinan tatace.

"Allah Sarki da jiyama zan Kira ki saikuma gashi Yau kinrigani jiya"

"Bakomai wallahi "Safiya ta fada
"kode an Samu karuwa ne"

Murmushi Sapna tayi sannan tace  "Eh Jiya na haihu "

"wow Allah ya Raya me aka samu" Safiya ta Kuma tmbya.

"twinz ne matah"

"Aa lallai kice Kinsha aiki, Allah ya Raya manasu ya Kara lafiya sai nazo ganin yarana tukun"

hhhhh"Ameen Nagode Allah ya kawoki lafiya "

Sannan sukayi sallama.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Murna Safiya tayi sosai jin Sapna ta sauka lafiya, nan ta Kuma shiryawa Dan zuwa kasuwa ta Kuma Yima twinz siyayyah.


Bash Ne ya shigo gidan tare da zama kan kujera ko sallama babu.

Banza tayi dashi, Dan yanzu haushi yake bata.

tasowa yayi har inda take tare da rungumeta ta bayantah.

jikinta ta janye daga Nata tare da fadin  "ya isa Bash pls, Ka fitar mun daga gida"

kallanta ya tsayayi cike da mamaki.

"Safiya Ni kike cema na tafi na baki waje "

Rufe idantah tayi tare da fadin "tabbas haka na fada Kuma bana fatan Ka Kuma shigomin cikin gida na gaya maka"

Dariya ya kama yi harda rike ciki, sannan ya Kuma kallanta tare da nuna tah "Safiya lafiayarki kuwa qlau,Kinsan Dawa kike magana kuwa "

tsaki tayi tare da nufar hanyar kofar Dan bar masa dakin.

janyo ta yayi ta fada jininsa, tureshi tayi a fusace tare da Kwada masa mari sannan ta nunashi da hannu  "karka kuskura Ka Kara taba jikina na gaya maka..


mamaki ya kamashi sosai Dan yana ganin abun kamar wasa...







😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB* 💅🏻 🌷







*Written by Zeenaseer 😘*
[24/3 23:32] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳              ⚜          🌳🌳
🌳                                        🌳
                      👑👑
                         🌳
            *MARAICHI*❣
                     *NA*
     *Zainab Naseer Sarki*
         *(Zeenaseer 😘)*





9⃣4⃣




*••••••••••*Nakin ta fita ta barshi a tsaya.

Wajan data mareshi ya rike yana kallan kofar data shiga sannan ya murmusa ya fita daga cikin gidan.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Yaune ya kama Ranar da Bash sukayi zasu hadu da Salma akan taje gidansa, banyan ta Gama shirinta gaba daya tayi shiga cikin Riga da wando Wanda suka kamata sosai sannan ta saka duguwar abaya.

Bayan Tafita daga gida Kai tsaye gidan Bash ta nufah.

dama ya Riga yasan da zuwanta, yana zaune yana shan giya acikin falosnsa, gaba daya Safiya ta bata masa rai sosai gashi yana mugun santah Dan baya tunanin yi mata wani abun Illa hakuri dayake shirin batah.


Bayan Tashigo cikin gidan tayi parking Motar ta sannan ta shiga ciki.

Zaune ta ganshi gabanshi giyace da Kuma sauran kayan shaye shayansa idansa ya kada yayi jajir Dan tsabar shayuwa da yayi.

Zama tayi kan kujera tare da ajje Jakarta Tana kallan fuskarsa.

"Lafiya kuwa na ganka haka"
Salma ta tambaya

Ko kallanta beyi bah taci gaba Da abunda yake, Wayarsa dayake ta faman kiran Safiya har lokacin taki dauka ya Kuma daukota tare da Kira amma harta Katse ba'a daga bah.
Jifa yayi da ita ta fada wajan Salma.

Da sauri ta dauka Dan Mika masa, ganin number da yake kirani yasanya zuciyarta tafasa.

Kamar tayi kuka ta Kama kallansa,cikin Ranta ta Fara fadin  '"kenan Duk wannan abun da yake Dan Safiya ta bata masa yake kenan, tabbas tafini a wajansa, Toh me take masa?"

ta tambayi zuciyarta Yayin data bata amsa da  "ta mallakamasa komai Nata shiyasa ta fiki "

tuni tayi tsaki tare da gyara zamantah, inde kuwa hakane Ni  "Salma nayi alkawarin mantar da Bash ya sanma wata Safiya cikin rayuwar Sa.

shikuwa sai faman bankar kayan shaye shayansa yake.

mikawa tsayi tayi tare da cire abayar jikintah, nan kirar ta tabayyana awaje gaba daya saman rigar kamar babu Dan ana ganin na fulanin tah.

Ahankali ta Fara takunta najan hankali ta karaso wajansa Tana karairaya.

Shikuwa barin Duk abunda yake ya tsaya yana kallan tah, Dan sak! Safiya yake gani bah Salma bah.

Zama tayi kan ciyarsa tare da saka hannunsa ya zagaye kuguntah tare da Fara romancing dinsa.

hakan yasa yaji dadi Dan gani yake kamar Safiya ce ke masa.

Tun daga haka yakai sun koma daki, suka ci gaba Da shashancinsu.




Bayan sun dawo daidai Bash baccinshi yayi,yayin da ita Kuma take kwance kan kirjinsa take tunanin yanda zata raba Safiya da Bash din.
   Dan tasan mundun suna tare da Safiya Toh babu musu zai iya barinta Dan taga ya mutu kan San Safiya.
  Tana cikin wannan tunanin bacci ya dauketa itama.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Bayan Safiya ta bar wajan Bash dakinta ta koma ta Kama kuka tare da rokon Allah ya yaye mata abunda tayi abaya sannan ta nufi toilet tayi wanka ta shirya ta nufi kasuwa.

Bayan taje tayi siyayyh da zatayi kaya masu ywwa komai ta gani ta daukoma Sapna Da yarantah.

Bayan Ta Gama gidan ta nufo Kai tsaye Duk da gabanta na faduwa Tana tunanin kar Sapna ta Rama abunda tayi mata abaya.

Tana isowa tayi parking sannan ta kwaso kayan ta shiga dasu ciki.


♣♣
Sapna na karamin Falo ita da Shaheeda da Zee Tana bawa Hanansa mama, Yayin da Hulud Tana Bayan Aisha suna Dayan falon da sauran jama'a suna hira.

Da sallama ta shigo cikin dakin.

zama tayi suka gaisa dasu Mamah, kasan cewar Tun suna yara rabanda mama ta ganta shiyasa bata ganeba amma tana mata kallan sani.

"Dama wajan Sapna nazo "

Allah Sarki Mum ta fada, Aisha rakata wajan Sapna.

kayan ta tayata dauka sannan suka shiga dayar kofar zuwa Dayan falon.

da sallama nan mah suka shiga.

sannan Aisha ta nuna mata wajan zama

lokacin Sapna ta Gama bah Hanansa Nono ta mikata wajan Shaheeda tana gyara rigarta ta Kalli Safiya.

itama Safiya kallanta take.

Murya na rawa ta furta"S..a..Pna "

itama Ahankali ta furta "Safiya "
da sauri Sapna ta taso tare da rungumeta Tana murnar ganin er uwar Tatah.

kowa kallansu ya tsaya yana yi,

"Safiya dama kina nan, dama zakizo wajena Eh Safiya? "

Safiya kasa magana tayi banda kuka babu abunda takeyi tana gyada mata Kai.

Da sauri ta kamo hannunta tare da shiga Dakinsu Mamah Da Itah "mama ga Safiya tazo wajena, tazo ta ganni"
Sai faman murna take tana hawaye.

Mamace ta Mike zaune tare da Kama Safiyan "Allah Sarki Dan uwa me dadi, Ashe kina nan Allah yayi muku albarka kinji"sannan Itama ta rungumeta.

kowa kallo yake sai tausayinsu akeji.

itade Safiya babu baki, kuka kawai take saboda nadamar da take faman damuntah.

haka Sapna kamar zata maidata ciki da soyayyah daki ta jata suka zauna sannan tace "Allah Sarki Safiya Ashe kina kaunata, kinga nayi aure harna haihu, nasan kema kinyi aure, ina yaran naki suke, ko baki taho dasu bah? Sai faman magana take tana dada murnar ganin er uwar Tarah.

Hawayan idanta ta goge tare da fadin "Nayi aure Sapna amma har yanzu ban haihu bah,"

"Allah Sarki Allah ya kawo masu albarka"

Ahankali ta zame daga kan kujerar tare da hada hannunta waje daya hawaye na zuba a idanta "Dan Allah Sapna ki yafemin Duk abunda na miki d..... "

Rungumeta tayi tana kukan itama"Babu abunda kikamin inma kim mim na yafe miki, Dan Allah kibar durkusa min kinji ya Safiya "

Kara rungumeta tayi tare da fadin "Nagode Sapna Allah ya Raya miki yaranki, ya baki zaman lafiya kida mijinki"

"Ameen yah" sannan ta zaunar da ita. "Bari akawo miki yaran naki "

Shaheeda ta kwalama Kira sannan ta shigo dakin "kawo ta"ta fada tare da amsarta, "jeki amso Hulud itama ta gantah.

"Shaheeda "Safiya ta kirata.

juyowa tayi Tareda da kallanta tana Murmushi,

Rungumeta Safiya tayi sannan tace "kin gane ni"

"gyada mata Kai tayi alamun Eh,

sannan tace "Ya Safiya ta Kebbi"

"Hakane kin gane ni, ya makarantah"

"Alhmdullh"itama ta fada.

Sapna sai kallansu take tana Murmushi sannanta  mikawa Safiya yarinyar.

itamakuma Shaheeda ta fita Dan dauko dayar.

"Kallanta Safiya tayi tare da fadin "Tubarkallah Allah ya Raya manasu"

lokacin Itama aka shigo da Hulud, itama amsarta tayi tare da musu addu'a, yaran sun shiga rantah sannan ta maidasu.

Kayan ta janyo tare da fadin, "Gashinan Kenakawoma da Kuma yarana"

"wow Gaskiya mun gode ya Safiya Allah ya Kara budi da Kuma kafin zumunci"

Nan ta dauki kayan ta kaima su Mum dansu gani Suma.

kowa kuwa ya Yaba da kayan sai godiya ake matah.






Hunin ranan Safiya agidan Sapna tayishi, sunsha hira sannan tare sukaci abinci.
   saida Safiya tayi sallar magriba Sannanta tafi.
har wajan motah Sapna ta rakata sannan ta tafi.

*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Lokacin da Bash ya farka daga bacci yaga Salma yayi mamaki sosai sanshi yama manta abunda ya Fara, amma yaji dadin ganin ta saki jiki dashi.

wanka yayi sannan ya fita ya siyo masu abinci.

Lokacin daya dawo har Salma ta gyara mashi dakin nasa.

Bayan sun Gama cin abincin. soyayyarsu sukaci gaba dayi har magriba tana gidan Bash.

Da ker ya barta ta tafi Dan yaso ta kwana dande taki yarda Ne sabo da Abbansu.

sannan ya sanar mata data rinka kawo masa ziyara dan ya daga tafiyar tasa sai next month...






😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL  FAN'S CLUB*💅🏻🌷





*Written by Zeenaseer 😘*
[24/3 23:32] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳             ⚜           🌳🌳
🌳                                        🌳
                    👑👑
                       🌳
          *MARAICHI*❣
                    *NA*
    *Zainab Naseer Sarki*
        *(Zeenaseer😘)*





9⃣5⃣




*••••••••••*Akwana atashi babu huya wajan Allah Yau yakama kwana 5 biyar da haihuwar twinz Wanda ya kama gobe suna.

Jama'a kuwa sun cika agidan en Katsina, kebbi da Kuma en nan bauchin Wanda suke a nesa.

Dan su Anty Rahma,Hafsa,su Anty ummie da Kuma matar Dan asabe shima har barka yazo sai Kuma Husnah kawar Sapna.


Me jego da Kuma yarantah kullum cikin kulawa suke sunyi kyau gwanin sha'awa.

Safiya MA kullum anan take huni sai dare take tafiya sannan tabawa Sapna labarin Kamal Itama Tabata Nata sannan Safiya ta sanar musu da basa tare dashi yanzu haka.

Sosai Sapna ta tausaya mata sannan ta ci gaba da addu'ar neman yafiyar abinda ta aikata.
    Amma taki sanar mata dasu suka aikata mata abunda aka mata gudun kada Sapna da sauran en uwa su tsanetah.


jama'a Duk suna Falo WASU Kuma suna can suna aiki.

Sapna kuwa Tana daki tana bama yarantah Nono.
Safiya Kuma tana sallar issha.


Bayan ta kwantar da Hanansa ta dauki Hulud Dan bata itama.

Shaheeda ta shigo dakin tare da fadin " Ya Sapna kawo tah na goyata inji Mum"

"sai de ki dauki Hanansa, Hulud bata gama sha bah"

Ahankali ta matso tare da daukar tah sannan ta fita da itah.

Lokacinne Safiya ta idar da sallar.

Sapna ce ta kalletah tare da fadin "ya Safiya kinki yarda amiki kunshi kowa an masa kinga keman dakinyi kyau"

Murmushi tayi tare da shafa addu'ar sannan tace "Sapna bana jin dadi wallahi bana san kunshi haka nan kwana biyun nan ganinan ne de"

Cike da tausayin yayartata, ta Kuma kallanta tare da Kuma fadin"Nima Naga kindan fada,kije Asibiti mana"

"Nima abunda nayi tunani kenan insha Allah Bayan sunan zanje bara kiga natashi natafi gida"

"Aww!  Wai da gasken bazaki kwana nan din bah Yaya "

"Sapna goban da huri zan shigo insha Allah pls Karki damu "ta karasa maganar tare da cire wayarta daga jikin caja sannan ta saka cajar ajaka.

Wayar Sapna ce tayi ringing Sannan ta dauka tare da mikama Sapna.

ganin Fahad ne ya sanya ta daga tare da Murmushi,

"ki fito ina waje pls"kawai ya fada tare da kashe wayar.

Mikawa tayi sannan tace da Safiya "ga Hulud pls yanzu zan dawo"

Amsarta tayi tare da fadin "so de kike nayi dare abeg ki maza ki dawo"

Murmushi tayi sannan ta yafa mayafinta ta fice ta kofar Baya Dan kar Mum ta gantah.



yana zaune cikin motarsa yana jiran fitowarta. ganin ta taho ne yasa ya gyara zamansa yana kallanta harta karaso ya Bude mata kofar ta shigo sannanta Rufe.

Cike da Murmushi Tajuya tana kallansa. Rungumeta yayi sannan yace "keman ko nemana bakyayi Mum ta zugaki ko? "

tana kwance ajikinsa tayi Murmushi tare da fadin "kaima kasan bazata bari mu hadu bah Tun rannan shiyasa tace karta kara ganinmu tare saide waya"

"hmm! Ai shikenan nasan de komin daran dadewa dole abani matata"

Dariya Sapna tayi tare da janye jikinta daga nasa tana kallansa.

janyota ya kumayi tare da fadin "kiyi Dariya dakyau zaki dawo ai "

"Toh na dena,nima ai ina missin dinka"

kiss ya manna mata akanta "Nasani soulmate, ina twinz ina suke? "

"sune missin Pappa dinsu "

"shima yana missn dinsu.

"Soulmate babu abunda kike bukata ne"

"Babu komai Allah ya saka da alkhairi ya Kuma Kara budi"

"Ameen ya fada sannan ya Fara neman bakinta ya Hada da nasa,ya jima yana kissing dinta ganin ya Fara huce gona da iri ta tureshi tare da fadin gudnyt"sannan ta fita daga motar tana Dariya.

ajjiyar zuciya a ajje sannan ya jingina kansa da kujerar.
shima Murmushi yayi me sauti sannan ya yima motar key yabar gdn.

Lokacin data shiga dakin ta tarda Safiya tana shirin kwantar da Hulud din Dan tagaji da jiran tah.

kallan tah Safiya tayi tare da fadin "Wlh da tafiya zanyi,kinje kin biyema wannan Romeon mijin nakI, saina gayawa Mum"

Dariya Sapna tayi tare da fadin, "Allah baki hakuri basai kin gaya matah bah"

"Muje na rakakin tunda kinki kwana "Sapna ta fada.

Gaba tayi sannan ta fita tayi musu sallama ta tafi har cikin motar tata Sapna tashiga sannan ta kalletah.

"Sapna Kara dare kike sani inayi"

Rungumeta Sapna tayi sannan tace "Ya Safiya pls ki kwana gani nake In kika tafi kamar bazaki dawo bah"

Murmushi tayi me sauti sannan tace Nima hakan nakeji amma babu komai insha Allah gobe around *10am* zan shigo sannan sukayi sallama, har ta fita da motar tata Sapna na daga matah hannu.




Lokacin da Safiya ta isa gida kasa koda canza kayan tayi ahaka ta kwanta.
Sabo da batajin dadin jikintah.


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Washe gari yakama assabr Wanda yayi daidai da Ranar sunan yan biyu wato *Maryam Hanansa* da Kuma twinz sis inta wato *Halimatussadiya Hulud*

Bayan sallar asbah akayi musu hudubah sanu amasallaci sannan da safe aka yanka musu Rago har guda biyar sannan Dad yasa aka yanka Sa.

Abinci kuwa Kala Kala da abun sha sai Wanda Kaga dama.
  Anyi kayan rabo rinsu Jaka, atamfah, kayan plastic, roba, bucket etc, dukkan abubuwan pic din yaran da Kuma sunan sune jiki harda calendar.📅

Nan danan gida taya fara cika da jama'a wajan *2pm*kuwa ba'a magana Dan jama'a dankar acikin gidan.


Dan harda en cikin *Ummiejay grp,01Amal fan's club, hamagee grp, momies gurl grp, Fahsap's grp, mj grp, matan so, Hausa nvls* Duk nagansu wasu nacin abinci wasu Kuma na rawa wasu na pic da twinz, *exquisite writers* kuwa Wanda sune manyan baki, suna zaune wasu na daukar pic da Sapna.





Sapna kuwa tunda ta tashi batajin dadin jikintah, gashi har yanzu Safiya bata zo bah, Takira wayarta akashe Tama rasa abunda ke mata ddi komai tana yinsane da sanyin jiki.






😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB 💅🏻🌷*






*Written by Zeenaseer 😘*
[24/3 23:33] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳           ⚜             🌳🌳
🌳                                        🌳
                    👑👑
                       🌳
           *MARAICHI*❣
                    *NA*
    *Zainab Naseer Sarki*
       *(Zeenaseer 😘)*





9⃣6⃣





*••••••••••*Tunda Jiya Safiya zazzabi ya saukar mata,da ker ta ke iya tashi.
   Haka ta daure wajan *1pm* tayi wanka tunda Tasha magani ta danjidadi.

Bayan ta Gama shirinta Dan tafiya gidan Sunan Dan tasa in bataje bah, Sapna bqzatji dadi bah.

Tana Gama shiryawa ta Dauko  cup da Kuma wani lemon mango dayake sanshi ta zuba tana cikinsha akayi knocking kofar tah.

Mikawa tayi tare da Bude kofar, Salma ta gani tsaye bakin kofar tana Murmushi taci Uban kwalliya kamar Wanda zataje gasar sarauniyar kyau.

Murmushi Safiya ta mata sannan ta bata Hanyata shige.

Zama tayi kan kujera sannan ta zauna Itama ,gaisawa sukayi sannan Safiya tace "Salma an zama manyan kasa ko neman Mubama ayi"

"Haba de yanzu gashi nazo dama shigowa nayi mu gaisa Dan saurima nake ina da wajan zuwa"

"Allah Sarki na gode bari na dauko jakata da Kuma mayafi nima dama fita zanyi"tana gama fadin hakan ta Mike tare da nufar damuntah.

Salma na ganin Safiya ta shiga Dakin tayi maza ta dauko wata er karamar Kwalba daga jakarta tayi maza ta juye wani farin ruwa dake cikin tah, a lemon Safiya sannan ta maida kwalbar jaka.

tana fitowa daga daki tace da Salma, "nama manta ban miki tayin lemo bah"

"Aa kibarshi nama koshimuje"sannan ta Mike ta nufi hanyar fitar.

lemon ta sanya a fridge sannan ta shanye sauran na cup din data rage ta Kai cup din kitchen, fita sukayi sannan ta kulle kofar ta sanya key din cikin jaka.

ganin wayarta na haske tayi maza ta dauko kafin ta dauka ta Katse kiran, missed call din Sapna ta gani har guda *38* batamasan sanda wayar ta shiga silence bah.

kiranta tayi Kokarinyi amma babu kudi a wayar TaTa, tasan maybe Dan Sapna bata gantah bane takekira tunda sunyi da ita *10am* zata Je.

Haka sukayi sallama da Salma kuwa Yashiga motarsa yayi hanyar da Zaiyi.


Tana cikin tafiya cikinta ya Fara murda mata,amma saita daure taci gaba da driving din har ta kara Nisa kadan.
   ganin Cikin Kara daurewa yasa Tafara sauka daga kan titin.duk kokarin da take Dan ganin ta tsaida motar kasawa tayi harsaida ta bugama wani mutumi.

gaba daya ta fada kasan motar tana rike da cikinta bakinta kamfah na fitah.

mutanan dake wajanne suka lura da hakan sukayi sauran kawo mata agajin gaggawa,

amma kofar motar taki buduwa sabo da Takulle daga ciki gashi ko motsi batayi.

sunyi iyaya yinsu amma sun kasa buduwe har kusan *3pm* tana ciki, koda aka samo masu gyara da ker daya ya Samu ya Bude, ganin Halin da take cikine yasa suka dauketa sukayi Asibiti da itah.

Cikin sa'a kuwa likitoci suka Samu sa'ar amsarta.





Gaba daya Hankalin Sapna yakasa kwanciya har mutane sun gane rashin kuzarintah.

tunda ta sake shigowa daki Dan canza kaya tazauna.

kanta ko dankwali babu, gashin bata sa masa ribbon bah. Ya zuba gadan bayantah, wani Kuma Yasauko gaban kanta.

Hafsace ta Kuma shigowa dakin tare da fadin "Wai har yanzu wayar bata daga bah?"

kamar zatayi kuka tace "Wallahi kuwa "

"ikon Allah Kara kiran Nata muji, Allah yasa lafiya gashi babu Wanda yasan gidantah dama Yau mukace zasuje mu kwana Kuma tamaki daga wayar"

jikin Sapna a sanyaye ta dauki wayar ta Kuma dailing number tata.




Wanda suka dauko Jakarta Dan dubawa ko Tana da waya akira en uwanta, yana dauko wayar kiran Sapna yashigo, da sallamarsa ya daga kiran tare da fadin "Yauwa me wayar tadan Samu accident ne yanzu haka tana Asibitin bakin kasuwa wato *DARMAH CLINIC* sannan ya kashe.


Tunda Sapna taji namiji ya daga hankalinta ya Fara tashi, bare dataji abunda ke faruwa gaba daya gabanta sai bugawa yake da karfi.

ganin hankalin tah yatashi Hafsa ta Fara tambayarta, kasa bama Hafsa amsarta tayi, mayafi ta dauka sannan ta fita daga gidan.

Binta Hafsa tayi tana Kira, amma ina driver ta taso jikinta na bari ya tashi ya shiga motar,itama shiga tayi haka Hafsa.

Da gudu yaja motar yanda Sapna ta umar ceshi, kamar zasu tashi sama.

Sapna kuka takeyi marar sauti.

Ahankali Hafsa itama jikinta dayayi sanyin ta Kalli Sapna tare da fadin "Sapna make faruwane Wai?"

Hawaye na sauka ga kumatunta tace "ya Hafsa Accident Safiya tayii"

"innalillahi wa'inna illaihir raji'un "shine abunda Hafsa keta faman fadi.


kafin su isa Sapna ta Kira mutumin tare da sanar masa, ya fito waje yanda suna zuwa zasu ganshi.



lokacin dasuka isa, suka hadu da mutumin Kai tsaye office din likitan ya kaisu Dan en uwanta likitan ke bukata.

Bayan sun gaisa yayi gyara muryata tare da fadin "Wato maganar Gaskiya hajiya wannan patient da aka kawo babu wani maganar accident datayi, poison ne aka bata Kuma wallahi me muguwar illar, dan Gaskiya Wanda ya bata ba karamin mugu bane bama asamun irinshi anan sosai sabo da yana da muguwar illar Dan yanzu maganar da nake miki, kaso 60 cikin 💯,kayan cikinta sun lalace.

da sauri Sapna ta rike bakinta tare dazaro idanta waje, kukane ya kwace mata tare da fadin "Wallahi sun kashe mana ita wani mugunne Wayyo Safiya tah"kuka sosai takama kamar mahaukaciya.

Hafsace ta iya dauriyar cewa "yanzu Dr. baza'a iya mata aiki bah"

"Gaskiya bamu da kayan aiki, Inna ba Waje Za'afita da ita bah yanzu Kuma lokaci yama kure Dan da ker in zata Kai gobe"

"innalillahi wa'inna illaihir raji'un, shikenan baiwar Allah wannan wani mugunne da mata wannan aiki sabo da Allah me tamasa "kuka itama tayitakamayi.

"Dr kaimu mu ganta taimaka"

Mikewa yayi tare da fadin muje, haka suka bishi ko wacce na kuka.



kwance take akan gado kamar ba itabah cikinta ya kumbura abun tausayi.

Da gudu Sapna ta karasa wajanta tare da fadawa jikintah tana kuka "ya Sapna Bude idonki ki ganni Dan Allah, Sapna ce tashi kinganni "tana magana tana kuka.

Ahankali ta Bude idan Nata dayayi jajir dashi bakinta sai kumfa ke fitowa hawaye itama take, Dan Daker ta iya Bude bakin Nata "sap.. na ki yafemin Dan Allah, kinji kimim addu'ar Allah ya yafemin Dan allah Sapna, har Dani aka kusan kashekin lkcn cikin ki, kukane yaci karfintah tana San ci gaba da magana amma Harshan ya mata nauyi,

"ya Sapna bakimin komai bah, nayafe miki, Dan allah Karki tafi ki barni, Dan Allah yayyyyy"k😭


Hafsa kasa shiga dakin tayi sabo tausayinsu, waje ta koma taci gaba da kukan.

hannunta Sapna ta Kama, wani irin Abu take tayi zafin mutuwa baiwar Allah, itama kukan take har ran ya fita.
 sai Kuma ta tsaya cak!!  idanta abude cike da ruwa,

fashewa Sapna ta karayi da wani saban kukan, Tana kiran Safiya.

tsaye ta Mike ta hada Uban gumi gashinta Duk ya jike ya manne bayantah, hannunta na karkarwa ta sanyashi tare da Rufe mata idan Nata, ruwan cikine suka bigefan fuskarta har kunan tah.

Sannan ta fito waje, Tana tafiya hawaye nabin fuskarta tah, jikinta Duk ya mutu, Tana fitowa Hafsace ta karaso tare da rike kafadun tah tana kallan bakintah dake furta "ta mutu !!" Ahankali, bakinta itama tayi maza ta toshe Dan kukan daya taho mata.

Rungume juna sukayi suna kukan.






*Ni kaina saida nayi kukan*😭😭




😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL  FAN'S CLUB  💅🏻🌷*






*Written by Zeenaseer 😘*
[24/3 23:33] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳            ⚜            🌳🌳
🌳                                        🌳
                    👑👑
                       🌳
          *MARAICHI*❣
                 *NA*
   *Zainab Naseer Sarki*
       *(Zeenaseer 😘)*






9⃣7⃣






*••••••••••*Saida sukayi kukan me isarsu sannan suka tambayi Dr.ko zasu iya tafiya da gawar,nan yace ba matsala, Sapna kuwa tace gidan tah Za'a Kai Safiya haka Hafsa ta hakura ta Rabu da itah.
    Nan kuwa yasa aka dauko gawar aka sakata cikin 🚑 sannan tabi bayan su, suna cikin mota ta Kira Fahad ta sanar masa, dakuma izinin tana San ayi jana'izar ta agidan su.
   Ba musu ya yarda Dan Duk abunda Sapna take so shima yana sansa.

Tunda aka fadin maganar accident din Safiya Sapna take kuka har kawo I yanzu.

Waya ta Kuma Kira can gidan suna, Suma aka sanar musu, sannan tace su taho gidanta.
  Nan kuwa aka hau jimami, Shaheeda ma kuka take haka Su Anty Rahma Dan mutane da yawa sunji mutuwar safiya.

Lokacin da suka isa gidan haka aka fito da ita aka shige cikin gidan afalo suka ajjetah.

Sannan Suma suka tafi.

Da sauri ta fito daga motar tare da rungume fahad tana kuka. "is OK Soulmate ya isa haka, addu'a yakamata kina matah"

"Hubby Safiya tafah, tatafi, bazan Karaganin taba 😭"Kara kankametah yayi ajikinsa yana lallashinta Dan ta Gama fita daga haiyacinta shima kansa tausayi take bashi Dan babu Wanda ya kaita jin muguwar.

jantayayi suka shiga cikin gida Hafsa na zaune zan kujera tasa Safiya agaba tana kuka tana mata addu'a.



Ba'a jima fah saiga su Mamah, dasauran jama'a Hanansa na Bayan Aisha ita Kuma Hulud tana Bayan Shaheeda.

Haka suka shigo gidan Duk jikinsu yayi sanyi.

Fahad kuwa daki ya saka Sapna tare da kwantar da ita muryata harta Dashe haka idanta sun kankance sunyi jajir.

Sannan ya fita dan gayawa jama'a ayi mata sallah da limamai.


Suna shigowa aka kaita wani daki Dan ayi mata wanka.

mama da Auntyummie ne suka mata wanka Sannan suka Gama shirya ta.

Aka fito da ita Falo. Sannan aka Kira jama'a Dan Akuma mata addu'a kowa kuka yake abun tausayi.

Shaheeda ce tataso Sapna itama Dan ta mata addu'ar suyi sallama.

Tana zuwa ta Rungume gawar tana kuka"dan Allah karku tafi da ita ku taimaka Safiya ta Dan Allah, kowa tausayin Sapna yake ji sabo da yanda ta koma.

Ana daukar gawar itama Tamike tana daga Mata hannu har aka fice da itah.

gaba daya taji wani iri Dan kukan MA yaki zuwa, sulalewa tayi kasa sumammiya.

Ruwa suka kawo aka zuba mata sannan ta tashi.

daki aka kaita aka kwantar Dan tasamu Hutu.

😔 *Allah sarki mutuwa me yankan Kauna,me raba masoya, me raba d'a da mahaifi,in tamu tazo Allah sa mugama da duniya Lafiya Ameen*😔


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Mutumin da Kamal ya yarda dashi ya gama cin amanar sa, ya kwashe masa kudin account dinsa gaba daya ya gudu.
   gashi en sanda sun kama Leon sabo da asirinsa ya tuno, gidan kuwa ya Sa aka moye masa Kamal Duk mutanan daya sa gadi sun gudu babu kowa.

haka kamar yake zaune acikinsa Dan ranan dayaci abinci ya kusa 9dys ko mutsin kirki Baya iyawa babu sallah ba sallati ya rame iya Rama yayi baki idansa Duk sun fada sabo da Rama.

ko hannunshi Baya iya dagawa sabo da yinwa gashi babu ta inda zai gudu ya gwada Tun yana da karfinsa harya gaji.

 Yana nan akwance ba umm babu um-um,


*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Yau kwana uku kennan da Mutuwar Safiya,sapna Duk tarame ta lalace kamar ba itaba, abincima sai mama tayi dagaske haka yaranma da ker take basu Nono, komai Nata ya tsaya cak ko walwala ta daina.


Bayan sadakar uku kowa Kuma yawatse, Mum ta hado musu komai nasu ta kawo musu Dan babu batun kowa, wata tsuhuwa aka kawo mata sai Kuma Shaheeda su kadai sukayi zaman su.

lokacin da Bash yaji muguwar Safiya har kuka yayi Dan yana Mugun santa Kuma har gida yaje yayima Safiya gaisuwa Duk da ta Ganeshi.

sannan sun Nemo gidan Safiya sunje sun gani.


*BAYAN KWANA ARBA'IN (40*

Lokacin anyi sadakar 40wa mutuwar Safiya,yaran Sapna sunyi wasu sun bulbul dasu gwanin sha'awa.

Dan yanzu gidan babu kowa daga Sapna, Shaheeda sai Kuma twinz.

Haka suke rayuwarsu cikin farin ciki, datayi 40har kebbi da Katsina sukaje suka danyi kwanaki.


Alhmdullh yanzu kam rayuwar farin ciki suke amma har yanzu Sapna inta tuna Safiya sai tayi Kwallan.




Kamal kuwa har ya mutu cikin wannan gidan Duk tsotsi suka cikashi ya kumbura ya fashe, sai doyi yake, daza'a gyara wajan wasu sukaga gawarsa aka sa aka dauketa aka akai bula aka yanda tah.

shikenan rayuwar tashi yayi muguwar hula kanci, Allah yasa mudace!



*^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^*
Salma kuwa tun Bayan data kashe safiya,hankalintah ya kwanta ta zama tauraruwar Bash Dan har gidansa take zuwa tayi kwanaki acewarta taje wata kasar agida.


Yauma Bash ya fita da dare tana gidan nasa tace tayi tafiya agida, Tana kwance daga ita sai part da bra sai Kuma wata milk din Riga doguwa Wanda bata da maraba da naked.

Misalin *1am* tana kallan bluefilm.
Kara Bude kofa taji.

A tunanintah Bash ne shiyasa batayi kokarin tashi daga kan kujerar bah.

ganin mutane tayi Manya Manya gardawa wajan su goma, kownne da mamaki ahanunsa.

Atsorace ta tashi zata gudu daya ya daka mata tsawa, babu shiri takoma ta zauna tana kallo.

"Wato abunda kike bukata shine kika zauna kina kallo koo"

girgiza Kai tayi tana hawaye.

Dayanne yace "ina mijinki"

"b.. B.. Babu.. B. Nni da miji,"

"wow kenan zaman kankiki kike yayi kyau"

"tashi kimana rawa to"

kuka ta Kama tare da rokwansu suyi hakuri"

"kee! Zan fasa miki Kai da 🔫, tashi "Dayan ya Kuma daka mata tsawa.

bashiri ta Mike ta Fara rawa tana kuka.

nan suka Kama Dariya suna kallanta.

daya daga cikin sune ya shigo kicin babu wani abinci, fridge ya Bude ya dauko kwalaban giya masu tsada ya kawo musu.

ogansu sune yace Gaskiya yarinyar nan ta hadu irin wannan abubu masu tsada da kike sha.

saida suka caje gidan Suka kwashe kudin gaba daya da Daduk wani Abu Mai tsada.

sannan ogansu yayi rape dintah.

sannan suma gaba dayansu saida sukayi, Tun Tana kuka harya zamto bata iya ko motsi harda masuyi abayan ta suka mata kaca kaca sannan suka mata dukan tsiya da wani katan gora,saida sukaga ta daina motsi sannan.
sannan sukayi tafiyarsu.








😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S  CLUB 💅🏻🌷*






*Written By Zeenaseer 😘*
[24/3 23:33] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳             ⚜           🌳🌳
🌳                                        🌳
                    👑👑
                       🌳
           *MARAICHI*❣
                   *NA*
    *Zainab Naseer Sarki*
        *(Zeenaseer 😘)*






9⃣8⃣




*••••••••••*Lokacin da Bash ya shigo gidan da sassafe, ganin kofar gidan abude yayi mamaki, shiga cikin gidan yayi yaga kwalban giyansa ko ina GA Salma kwance tsirara cikin jini.
    Mamakine ya kamashi, cikin dakin ya shiga ganin an kwashemai kudinsa yasa ya fito daga dakin a fusace,tashinta yakiyi amma yaki tashi kitchen ya shiga ya ciko bukiti da ruwa sannan ya Shara mata gaba daya.
Azabure ta tashi tana kallansa. Kafin ta Kuma fashewa da Kuma idanta daya ya kumbura Sai ruwa
Yake.

"Uban waye ya shigo gidan nan ya daukarmin kudina"

"Haba Bash bazama Ka Kalli Halin da nake cikivah kaita kudinkama kake"

"tohni ina ruwana ko kasheki Za'a yi babu abunda Yadameni Kuma wallahi Sai kin biyani  kudina.

Da ker ta lallaba ta saka rigarta me nuna tsiraici tana kokarin tashi amma ta kasa.

Janta yayi Yakaita mota sannan ya dauki ATM dinta ya tafi da ita.

"Haba bash Baka da hankali kagafa kayan dayake jikina zaka fito Dani"

kwada mata mari ya karayi daidai wajan idan dake tsiyaya "ashar ya kundima mata, zanje na cire kudin dake account dinki Nikuma be kaiba zan kaiwa ubanki yamin ciko.

Kuka ta Fara tana rokansa karya Kaita gida amma ko ajikinsa.

Yana zuwa kofar gidan yabude motar tare da turata tafada waje.

wani ihu ta saki Sannan yaja motar yabar gidan.

Kan kafar dake mata ciwo ya jifarta.


Ihun tayine yasa me gadinsu fitowa da sauri.

ganin Salma kwance yasashi dora hannu aka tare da shiga ciki da gudu, Mamah, Abba da  Zuly suna falon suna hira me gadi ya shigo da gudu tare da fadin "Alhaji an kawo yarinyar wajnka wallahi babu kyangani ko taimaka mata jama'a na hucewa"


Da sauri suka fito Dan ganin abunda ke faruwa, turuss!! Sukayi kofar gate ganin Salma cikin Halin da take.

Gaba daya mamaki suke, ita kuwa kanta akasa sai kuka take.

Mamah ce tayi wajanta tana kuka zata taimaka mata.

Tsawa Abba ya daka mata, cak ta tsaya "wallahi kika sake kika Tabata nasakeki saki uku, ke Kuma Duk tarbiyar da muka baki, Da wannan hulakancin zaki saka mana, wallahi ban yafe miki bah, Allah ya isa tsakanin mu dake, Kuma ke ba yatabace nabarma duniya ke"
Yana kaiwa nan ya juya yana kuka, ya kama hannun Mamah da Zulaihat suka shige gida Suma kukan suke.


kuka Salma taci gaba dayi har Yamma tana zaune ga kafa da ido suna mata ciwo.



Motar police ce tayi parking kofar gidansu,da yake qkwai haske wajan ana ganin tah.

Har zasu shiga gidan tare da wasu mutane su uku daya daga cikinsu yace "bama Saimu shigaba Gatanan ya nuna Salma dake zaune kamar almajira yinwar dake cikintama ta ishetah,

"Itace officer saida ta damfaremu 20millons kowanann mu Dan haka dauketa harsai kudinmu sai fito asaketa"

tana kuka idanta na ruwa haka suka sata amota suka tafi da ita.





Bayan sati uku da kaita gidan yari kafarta ta rinka ruwa dama tuni ido daya ya tsiyaye haka aka kaita asibit aka yanke kafar daya, sannan suka maidota gidan Yarin taci gaba da rayuwa har karshen ta.




Shikuwa Bash kudinsa ya kwashe gaba daya sannan ya tafi gida. Yana cikin tafiya yana murna.

Wata Babban mota tabi takan kanshi gaba daya kan nashiya rabo da huyansa. Ya gaggara kan titi. Shima me motar ya gudu haka suka daukeshi ko wanka babu suka bunneshi acikin wani kango da kayan jininsa.


haka suka kashe kudin nasa gaba daya daga amso suka gudu dasu.







*BAYAN SHEKARA BIYU*



Gidan Fahad suna cikin jin dadi Da farin ciki yaransu sun girma sunyi wayo babu inda bazasu da kafar suba gasu da baki GA barna bare aka ce Hanansa tafi kowa Dan ita Hulud bata da kiriniya sai Rigima.

Sapna kuwa ana ta fama da tsohon ciki Dan takusan haihu.

ana yawan kaisu wajan Mum amma suna shan barna da rashin ji. ita kuwa mama bata yarda su kwana Dan basa barinta tayi bacci ga shan shayi komin dare saita hada musu sunsha.

itama Shaheeda an kusan bakinta Dan baifi wata biyu bah Zee kuwa harta haifi danta namiji.

zumuncinsu ya Kara karfi Dan kowanne yana kokarin faran tama Dan uwansa.

♣♣
Fahad yana zaune suna hira shida Soulmate dinsa afalo Yayin da Shaheeda da twinz suna daki.

"Hubby nafa kusan haihuwa Danna matso na sauke na huta"

"Haba soulmate abunda yanzu kika Fara Haifa mana, sonake mu Samu kamar guda 10 haka koya kika gani"ya karashe maganar tare da daga Nata girah.

Dariya tayi Sannan tace "uhmm! Dan bakai Kake haihuwar bane shiyasa Kake wannan maganar amma dakanayi bazaka fadi hakan bah"

"Kina nufin kenan kin fini karfi da dauriya"

yanda kace amma kasan da huya ai.

rungumeta yayi tare da fadin "Nasani Allah ya saukeki lafiya ya Kuma bamu masu albarka I love you "ya fada"

"lov u more "itama ta fada tare da Kai bakin ta kan nasa Hulud ta fito daga daki tana kuka.

kallanta suka shigayi harta karaso tana kukan Fahad Ne ya dauketa tare da fadin "ohhh! Waya tabamin Bbyna am sowie"ya fada yana goge mata Hawayan.


"Pappa"ta fada tana kallansa tare da turo baki cikin shagwabah "Hananca dole shetamin kwallinyah miko banacho chine ta cijeni"

kallan hannun yake inda ta cige tan.

itama sai Gatanan ta fito daga dakin taci Uban kwalliyar hauka, Duk ta bata fuskarta da kwalli da Kuma Jan baki powder har cikin gashin kanta da aka musu kalba guda biyu.

kallanta suka tsaya yi ita kuwa ko ajikintah takalmin Shaheeda ne kafarta sai Kuma Jakarta tAh.

kamar Sapna tayi kuka yanda suka bata jikinsu.

tashi tayi tare da shigewa dakin Fahad ta barsu wajan Fahad.

kallanta yayi tare da fadin "Bbyna Kalli yanda kika koma kamar dodo, zo muje a goge "

make kafada tayi tare da fadin "gidan Mum zani" dama itace zabiya uwar iya magana.


"naji bara awanke kwallinyah sai muje na kaiki"

"Pappa Nima jani" Hulud ta fada.
caraf ! kuwa Hanansa tace "Aa ba Za'a dake bah"

da ker Fahad ya lallabata aka goge kwallinyah ya musu wanka ya canza musu kaya sannan ya kaisu Dakinsu ya kwantar dasu ya lallabasu sukayi bcci kulle dakin tayi Bayan yamusu addu'ar sannan ya tafi daki.


yana shiga ya kwanta tare da janyota jikinsa, har kinyi bcci,

aaa inasan shirin yi, hayaniya yaran Ka yahana Ni, Kuma abun haushi Shaheeda tana can Tana faman banzan wayanta suyi barna bata sani bah.

yade isa ya fada sannan suka kwantah..






😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL  FAN'S CLUB 💅🏻🌷*






*Written by Zeenaseer 😘*
[24/3 23:33] Hussaina: 🌳🌳             ⚜           🌳🌳
🌳                                        🌳
                     👑👑
                        🌳
            *MARAICHI*❣
                   *NA*
     *Zainab Naseer Sarki*
        *(Zeenaseer 😘)*



9⃣9⃣




🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀
*Dedication to you mother, ur d best Mamah, I love you ❤😘*
       *I Swear my love for you will never end*😍
    🌺🌺
    *Wish you success nd long lyf Mamatah*☺
🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀



⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜
*••••••••••••*Tun daran Sapna ke nakuda, da asbah suka tafi asibiti, karfe *7am* daidai ta haifi santaleliyar yr tah Wanda tafi su Hanansa kyau ga Suma tubar kallah.

Murna wajan Fahad ba'a magana, Alhmdullh ta haihu lafiya Dan haka bata wani jima bah aka sallamusu suka dawo gidantah,nan aka rinka zuwa barka.


Ranar suna yarinya taci sunan Safiya amma suke kirantah da *Mimerh* yarinya kyakkyawa gashi bata da rigima haka su Hanansa suna kaunarta ko kiriniya suke da ance Mimerh ta bata daku zasu nutso.


Haka rayuwa farinciki da jini dadi ta kasance agidan Fahad shida yaransa da matar sa.


Bayan tayi 40,aka Fara bikini Shaheeda, sunsha shagali sosai Bayan Biki Angonta ya dauketa suka tafi UK dama acan suke.


Sapna kuwa an zama manyan mata, babu abunda ta rasa wajan mijintah da Kuma en uwanta shiyasa kullum cikin Kara godiya wa Allah take.


Tundaga lokacin nabar wannan family cikin farin ciki bani na sake dawo wa bah sai Bayan shekara *15* da sallama na shiga cikin gidan.

Yarinya budurwa nagani zaune saman kujera kyakkyawa Fara tas da ita tana Danna waya.

Wata Kuma na Kuma gani ta sakko daga upstairs shanye da Jean baki da red top, Ta tagyara gashin kanta sai Sheki yake ,ta karaso wajan wannan ta kwancan tare da fadin "ke Mimerh ke kika daukar min USB cable dina kk? "

Ahankali ta tashi zaune tare da fadin "Wai Dan Allah ya Hanansa da kin nemi abunki kin rasa saiki ce nice kamar nikadai ce cikin gidan"

"ohk hakama zaki ce "

Sapna ce ta fito daga daki tare da zama saman kujera ta kara kyau ta zama babbar mace, "Lafiya cweerie nah Waya taba min kenan? "Sapna ta tambayi Mimerh dayake Duk cikin yaran babu Wanda take so kamar ita., Tana da hankali, nutsuwa ga Kuma Kokari.

Kamar zatayi kuka tace "Ammie Wai Dan Allah data rasa abinta saitace Nina dauka matah "

kallan Hanansa Sapna tayi tare da fadin "Menene ake neman?"

"USB cable na aka dauka "ta bata amsa.

"Kamar Hannun Muhammad na ganshi dazu bari ya shigo"Sapna ta bata amsa.

Shine autah daga Mimerh sanshi shine kadai namiji, kyakkyawa ne shi kamarsu daya da Fahad dande yafi Fahad Haske.

Cikin fishi Hanansa tace "wallahi Ammie nakamashi saina koya Mai hankali,kullum bashi da aiki sai daukama mutun abunsa"

kallanta Sapna tayi kafin ta Kuma cewa "Bana hanaki irin wannan shigar bah? "

Shiru tayi sannan tace "Amma Ammie cikin gidane fah "

"kije ki canza Riga nagaya miki "


upstairs ta nufah tana gunguni Dan batasan saka manyan kaya itah.




Bayan Magriba suna zaune kan dining suna dinner, Fahad ya Kalli Sapna tare da fadin "Baga Hulud bah? "

"Tunda safe ta tafi wajan Mamah kasan dama bata jimawa bata jebah "


"Pappa ya maganar tafiyar tamu UK din "Hanansa tace wa Fahad.

"Bara Hulud din ta dawo sai ayi maganar da itah "

Muhammad Ne yace "Pappa Nikuma laptop din "

"Za'a kawo maka, katsaya kayi karatu kaji son "

"insha Allah Pappa nah"

Tunda suka Fara hirar su Mimerh batace Kala bah.

kallanta fahad yayi tare da fadin "Ameerah ba abunda Za'a ce Yau Kuma "dayake haka yake kirantah.

Murmushi kawai tayi Wanda yasa dimples dinta fitowa "Pappa Ni bana Bukatar komai "

Haka sukaci gaba da Hirar su cikin farin ciki.


♣♣
Bangaran Shaheeda mah tana cikin farin ciki ta haifi yarantah uku maza biyu da mace daya.
Ibrahim khaleel, Uthman sai macan Sapna suna kiranta da Iman.



*HAPPY ENDING*😎









🔚‼🎊🎊









😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*01 AMAL FAN'S CLUB*💅🏻🌷









*Written by Zeenaseer 😘*
[24/3 23:33] Hussaina: *©EXQUISITE ONLINE WRITERS*
🌳🌳           ⚜             🌳🌳
🌳                                        🌳
                   👑👑
                      🌳
         *MARAICHI*❣
                 *NA*
    *Zainab Naseer Sarki*
       *(Zeenaseer 😘)*





1⃣0⃣0⃣



🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻
*GODIYA TA MUSAMMAN TA TABBATA GA ALLAH SUBHANAHU WATA ALLAH, DAYA BANI DAMA, IKO DA KUMA LAFIYA NA RUBUTA WANNAN LITTAFI DA KUMA KAMMALASHI LAFIYA*


🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
*WANNAN LITTAFI NAWA BA LABARIN WATA KO WANI NA DAUKABA NAKE BAMA MUTANE BAH, NA KIRKIRI KAYANA DA KAINA, DAN FADAKARWA,NISHA DAN TARWA DA KUMA NI'IMANTAR WA*


🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀
*INA MIKA GODIYA TA GA MANYA AMINAI NA KUMA MASU SAN CIGABANA MASU KARFAFAMIN GWIWATAH, NAGODE SOSAI ALLAH UBANGIJI YA SAKA DA ALKHAIRI*

*UMMIJAY*
*UMMIKAY*
*FIYYA*
*MHIZDIJAH TAWAN*
*AXLAN*
*HOMEL*
*BELLZARAH*
*HAMAGEE*
*MUMSUDIES*
*MUMCYAMA*
*SHAHEEDA*
*BEELERH*
*OH JAANAA*
*MARYAM*
*AMEERAH*
*DA DUK SAURAN MASOYANA INA SANE DA SUNAN KU,NAGODE,NAGODE*

🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
*INA KARA GODIYA GA :*
*01 AMAL FAN'S CLUB*
*UMMIJAY GRP*
*HAMAGEE GRP*
*LADIES WIT CLASS*
*FAHSAP GRP*
*H N UBANDIYA GRP*
*HAUSA NOVELS*
*DIMPLES GRP*
*MF&J NOVEL GRP*
*MOMIES GURL GRP*
*MATAN SOO*
*FADILA LAMIDO GRP*

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
*GODIYA TA MUSAMMAN ME TARIN YAWA GA EXQUISITE ONLINE WRITERS, ALLAH YA KARA HADA KANMU YA KUMA KAREMU DAGA SHARRIN MAKIYA DA MA HASSADA*

💐💐💐💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
💐💐💐
💐💐
💐
*MASOYANA BAN MANTA DAKU BAH KUMA BAZAN TABA MANTAWA DAKU BAH,GODIYA TA MUSAMMAN DA TAFI TA KOWA KUNE JIGONA IN BABU,BABAH NI, BAZAN IYA MISALTAH IRIN FARICIKIN DAKE CIKIN ZUCIYA TABAH NAGODE SOSAI KUMA INA MUKU FATAN ALKHAIRI ADUK INDA KUKE, SO MUCH LOVE FOR YOU PEOPLE*❤



✨🌸🌸✨🌸🌸✨
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
✨🌸🌸🌸🌸🌸✨
✨✨🌸🌸🌸✨✨
✨✨✨🌸✨✨✨




☁💟💟☁💟💟☁
💟💟💟💟💟💟💟
💟💟💟💟💟💟💟
☁💟💟💟💟💟☁
☁☁💟💟💟☁☁
☁☁☁💟☁☁☁
*Love you muah.....*💋




😎😎😎😎😎😎😎😎😎😎😎
*👋 BYE-BYE*



💃🏻💃🏻
*TAKU HAR KULLUM*

*ZAINAB NASEER SARKI*
    *(ZEENASEER 😘)*

Web Web Design today in in cheaper price, Join our tech blog to learn some other things
adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *