Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Saturday, July 7, 2018

FULANIN DAJI Complete Hausa Romatic Novel

adsense here
FULANIN DAJI Complete Hausa Romatic Novel
9/27/16, 7:56 PM - Messages you send to this chat and calls are now secured with end-to-end encryption. Tap for more info.
9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: FULANIN DAJI
N@ B aleeyu  page 1
Joda! Joda! Joda! Wai kina ina neh haka Iye (anani) kinajina
gwaggo ina zuwa , Bankara she kwalliyar ba kinsan yau ance Yan bunni sunzo gwara muyi kwalliya da kyau,

gwaggo tace ke bana San shirme kizo kose dawon yayi karfi, tindazu kina abu guda , seda takare ranbade2 denta sannan tafito,   kungan joda kuwa yarinya har yarinya amma ta bata fuskarta da Jan baki da bakin kwalli ko ina digagga ne afuskarta rigarta da zaninta iri daya Dan kwalinta kuwa na irin tsofaffin nan ne

Rike da qugu tafito tana daga gira sama, gwaggo dubeni nayi kyau, gwaggo tace wlh da kina jin zancena dakin koma kingoge wannan haukar, buga kafarta tayi kasa ni wlh baxan goge ba, so kike Su hansai Su cemun bakauya, Gashi Yan bunni zasuzo

Gwaggo tayi murmushi shikenan zoki wuce, gyalenta tadauko tasha damara sosai, Yan kirgan Dan ginta suka Dan fito, gwaggo ta dora mata kwaryar dawo da nono akai, tana kara jamata kunne, banda shiririta fah,

har takai kofa sekuma naga Tajuyo tana kallan gwaggo duk tabata fuska , sanin abunda take nufi yasa gwaggo yin murmushi to allah ya kiyaye hanya yakare mun ke yamaidoki lfy, murmushin itama tayi ko kefa gwaggo daso kike inje can infada kogin kada, 

Hava autare ya daya tamkar da dubu gudaliya, yar fillo yarinya se mai rakumi koh, bushewa tayi da dariya aikodai gwaggo inyita hawa abuna koh, gwaggo tace sosaima kuwa kedai jeki maraice nayi,

Tana fita gwaggo tasa dariya inbahaka nayi mata ba, bazata sa yadda dawon ba gurin wasa zataje, sallama akayi, dasauri tamike tana sannu dazuwa sannu da zuwa mai gida,  hakin tasauke masa akansa, takarbi karan dake hannunsa ta ajiye,

Shimfida tamasa takawo masa fura mai sanyi taji nono, yasha ya koshi Alhamdulillah shine abunda naji yafada, (a kullum kada mu manta da hamdala ga ubangiji a duk lokacin da muka samu wata biyan bukata)

Kallanta Yayi allah Yayi miki albarka , dukadda kanta tayi kasa tana cewa ameen kaima allah yasaka maka da gidan aljanna mafificiya, ameen

Ina joda taje,  gwaggo tace ta tafi gurin talla, Yace Ince dai ko kin jamata kunne kada taje gurin Jan fada asace dawon tinda kullum seta batareda kudi, gwaggo tace to yazanyi da ita se addua ,baffa yace to allah yashirya mana ita ameen

 FULANIN DAJI
N@ B aleeyu page  2
Tafe suke itada hansai se rangwada suke, wai Su Yan mata ne, Duk wadda suka hadu da ita se sunbushe mata da dariya, Su aganinsu sunfi kowa haduwa

Hansai kawar joda ce atare aka haifesu kwana biyu ne tsakanin joda da hansai, an haifi joda jumu'a aka haifi hansai lahadi, Atare suka taso dayake makwabtane sedai mahaifin hansai yarasu daga baya yayansa ya auri uwar hansai din kasancewar sun rabu da tashi matar
         "Wannan kenan "

Dai dai kasuwa suka tsaya suna waige2 kozasuga wanda yazauna musu guri, babu kuwa hakan yabasu damar zarcewa gurin Su, arunfar mai shayi kenan, koshi mai runfar bai isa yahanasu gurin ba

Hansai ta fidda shinkafa da wake , joda kuwa tasauke, kwaryar akasa tafara damawa habu mai shayi, coz tasan wajibine kullum seya sha furar ta, hansai kuwa harta zuba masa shinkafar kamun yagama Ci, joda tagama dama masa fura da nono

Asslamu alaikum sukaji ance da bakuwar, murya habu mai shayi shine ya amsa,  hansai da joda kuwa sun mutu gurin kallan sa, wannan Dan bunnin kamar aljani,

Am not aljan am also man, haka sukaji anfada se a lokacin tagane ashe afili take zancen, kunya ta lullubeta dasauri tarufe fuskarta da mayafinta , murmushi Yayi ahhh ashe kinsan kunya, adamamun fura da nono asaka sikari amma,  kasa amsawa tayi se hansai ce tanawa,

Zare ido Yayi yace bansan kota nawa zance ba, adamamun kawai wadda zata isheni, se a lokacin tayi magana to ay bamusan cikinka ba, murmushi Yayi tokidama mun dai2 cikinki,

Dago idonta tayi tadora masa to kuma kasan ciki nane, ayku Yan bunni bakwa cin abinci dayawa, dariya yadiga yi harda hawaye  yana rike ciki, injiwa ayko wa da nasa personality din , nidai kawai kidama mun dai2 cikinki dts oll,

Dawo biyar naga tadakko ta zuba cup din, tafara damawa, kallanta yake yadda take aiki komai atsabtace, take yinsa, seda tagama sannan tazuba sugar ta naira goma tasaka masa ludayi aciki bayan ta sake dauraye shi,

Sha yake se zuba santi yake, yana fadan duk sokoto babu mai irin wannan furar, joda kuwa se dariya take zubawa ita da hansai, kadan2 yake shan furar wai bayaso takare, kafun nan har sun sayadda kayansu

Mikewa yayi yana karkade wandonsa dabadan karkice nayi santi ba danace, waiko da tsaba kuke wannan furar, aikuwa yade bowa kansa dariya haka Suka Dunkule Su biyu suna ta dariya

Tin yana biye musu har yafara tsorata Anya kuwa wadannan yaran lafiyarsu, habu mai shayi yace dena mamaki indai Su hansai ne wlh se sufi awa suna dariya bakomai bane agaresu

Ido yazaro yace  toh , ungo kudinki nikam tafiya zanyi dari biyar yamiko mata, ta ware ido, yo ay ko duka dawon na dari ukku ne balanta wanda kasha kaga kudinka hamsin da biyar ne fah, dariya yayi hava dai ace duk wannan dadin gashi cikina yayi dam ace 55 naira kawai kinga naji dadin furar kije kawai nabaki canjin yajuya abun sa

Saurin shan gabansa tayi, tana rufamun asiri wlh gwaggo tahanani yin juye ma balantana wannan kudin ni kabada naira hamsin nayafe biyar din 

 FULANIN DAJI
N@ B aleeyu  page 3
Yace to kinga tsaya ni banda canji ko dari biyu banida ,  joda tace to ka tsaya  habu yamana canji, batajira cewarsaba, taje tabawa habu kudin yayo musu chanji, seda takirqa Su cib sun cika sannan tacire kudinsa takaimasa ragowar,

Kudin yake bi da kallo duk Yan biyar biyar ne se goma goma can yahango hamsin guda,  cike da kyama yace miye wannan haka, joda tabude baki Au idonka baya gani ne kudinka ne mana , murmushi Yayi kinga kirabawa almajirai ni baxan iya taba wadannan kudin ba, kema idan kinje gida kiwanke hannunki da sabulu yana kai nan yajuya yawuce yabar joda rike da kudin

Hansai takaraso tana tanbayar ta lfy nan take gayamata yadda sukayi dashi, hansai ta washe baki Iye daga allah yabamu allah kizo muci kashin bature  (chocolate  )

Joda tace ke Dallah je can mai shegen kwadayi muka sani ko mubace idan muka Ci kudin , hansai ta ware ido hakane fah, Kinga muyi Gina muzuba kudin kawai, joda tace haka za'ayi ni har wadannan ma zubarwa zanyi,

Haka kuwa akayi sukayi gina dai2 wani dutse suka binne kudin, kowannensu tsoro yakamata, addua kawai suke har Suka kai gida,

Mahmud kuwa yana isa titi yatare Dan achaba se masaukinsu , yana isa yatarda dakinsu abude hakan yatabbar masa da cewa Ahmed na dakin, sallama yayi tareda cire talkaminsa

Ahmed ko kallansa baiyiba, yafada kan gadon yace man waya tabamun kai, Ahmed yaballa masa harara, zaiyi wata magana Ahmed yadaga masa hannu  don't tell me anything,

Mahmud yaji haushin abun amma kuma seya basar  , tashi yayi yabude fridge yadauko masa eviron drink , ya zuba a cup yabasa,  Ahmed baiyi wata2 ba yakarba yadinga sha gani nai kawai ya ajiye cup din, Mahmud yakallesa are you Okey?

Yeah am ok, nikam mamaki ya cikani ace duk fushin dayayi yanxu babu shi, ko miye dalili oho, Mahmud yayi gyaran murya yace my man kaci abunci kuwa ? Ahmed yabisa da harara naci wanda ka kawo mun  ,  dariya Mahmud yayi kaifa kace inje bazaka iya cin abuncin Yan kauye ba, so ni nasha furata mai dadi allah baka ganiba taji no.........shiru Yayi ganin yadda Ahmed yadafe bakinsa da hannushi , dasauri ya tashi yashiga toilet ya zubadda yawu,

Mahmud kuwa laptop dinsa yajanyo yashiga danne2 abunsa, bayan kamar minti ashirin, Ahmed yace Kainifa yunwa nakeji wlh, Mahmud ya hararesa mezan maka yanxu ? Ahmed yace bansaniba afusace, Mahmud yayi tsaki allah ya gyara maka zuciyarka Dan wlh kana cikin uquba, yakarashe zancen cikin fushi

Ahmed kuwa yajanyo bag dinsa yafiddo chocolate  cornflakes yahada da madara yasha a karamun cup, yazo yayi alwala yatada sallah abunsa, Mahmud yagirgiza kai cike da  takaici aransa yace zanga randa Ahmed zai gyara behaviours dinsa, yanxu yana nufin masallacin ma bazai jeba sedai yayi sallah gida

Bara muleka joda"
Tana shiga gida da sallamar ta, baffanta ya amsa, Dagudu taje tafada jikinsa tana (inballi jam baffa ) ina wuni baffa " ya amsa mata lfy lau yar baffa, ya kasuwa, lfy lau baffana, baffa zanyi sallah, Yace to joda kiyi sallar kwarai, ana bukatar natsuwa da ikhlasi azuciyarki, ki qudurta aranki kamar kina ganin allah ne gaki gashi kitsarkake zuciyarki kinji yata, murmushi tayi nagode baffa, zanyi yanda kace


Tagama sallah taje kitchen dinsu tadakko abuncin ta taci tasha sabon nono madara kenan, kayan jikinta tacire tasaka nazaman gida,  lekawa tayi taga bakowa awaje, tasaka talkaminta a hammata takwashe wandonta Sadaf2  take tafiya har takai kofa, anan taballa da gudu

Carab sukayi kabra da hansai itama ta tsero, rike hannunta tayi suka balbala da gudu se dandali, Koda sukaje har anfara kida, dama su barawa suke ba, Sedai suyi kallo sudinga tsegumin wasu

Mai fura taji anfada, dasauri Tajuyo dazummar fada domin ta tsani acemata mai fura,  wazata gani Dan bunni ne nadazu lah kaine tafada tana murmushi mekazo yi nan? ke mekika zoyi nan?

Wata yar Dariya tayi kallo mukazo yi mana, Yace kodai rawa kika zoyi, tace a'a wlh tadukadda kanta kasa, yayi dariya yayi fulanin usuli ansanku da kunya koh, hansai ta matso, Lah Dan bunni ne, Yace ke badan bunni sunana ba, sunana Mahmud,  Mey?  Joda ta tanbaya, yes it's my name , joda tarufe baki tab, Mahmud yace lfy kuwa, hansai tace sunan baffanta ne, hhhh ya aza dariya daga yau baba koh

Joda tace waima baba, Mahmud yace Au ban haifekiba, ta gwaguda baki kaima kasani ai,  yayi dariya yace to yaya, tace da dai yafi kam........

Muje zuwa
ASEEYAH BASHEER ALEEYU
9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: FULANIN DAJI
N@ B aleeyu  page 4
Yau alhamis ba'a zuwa makaranta, yaukuma Ranar da baffa yake zuwa daji se dare yake dawowa saboda kiyo shanun sa dayake dakuma gonakinsa

Joda ta shirya cikin kayan Su na fillo tasaka riga iya cibiyarta takawo zani ta daura tarufe cikinta sedan wani abu akan ta fuskarta cike da kwalliyar hauka anyo mata kitson nan na fulani manya2 tazuboshi ko ina baya da gaba

Gwaggo awalijam  ( ina kwana kenan ) ta amsa lfy lau auta kintashi lfy, joda tace lfy lau, gwaggo natafi, daji, gwaggo tace to yata allah ya kiyaye mun ke daga kowane mugun kwaro, joda Dan allah banda shiga ruwa kinajina,

Ta gyada kai to gwaggo insha allah lfy lau zan dawo baxan shiga ruwa ba in tsoron kogin kada, za gayawa tayi baya takoro shanunta biyar tika2 dasu gwanin sha'awa,

Kofar gidansu hansai ta tsaya ta tada mabusarta ta fulani tana busawa, hansai dake saka talkaminta tace ina zuwa joda Bara nasha nono, joda tayi tsaki kya sameni ahanya

Hansai tamaza tasha nonon taka do shanun ta, ukku suka biyo hanya kowacce da bulalarta suna dukan shanun Su idan sunbi hanyar da badai dai ba, hansai tace allah yasa muga Dan bunni joda,  joda tace mezai kai shi daji, tinda ba ma kiyayi neba , ahaka suke tafe suna fira har Suka kai daji,

Kowacce tabi tata hanya inuwar mangwaro joda tasamu tazauna, tafiddo furar ta tafara sha ' can kuma ta ajiye, tadauko mabusar ta tafara busawa,

Zaune yake bakin rafi yana sha kar iskan dake kadawa, yazanyo jacket dinshi yasaka busa yakeji natashi irin ta fulani, idonsa ya lumshe rabensa dayaji wannan busar tin mahaifiyarsa nada rai idan sunje kauyensu wato ba'are,

Haka yacigaba da sauraren busar can kuma yadaina jin busar,  ba afi minti goma ba yasake jin wata daban tamkar irin busar meminsa dasauri yamike tsaye yana bin gurin da yakejin busar har yakai wani guri!

Ba yanata kawai yake hangowa cikin kayan fulani yana kallan yadda take juya kanta ahankali tana busar, ko shakka babu wannan cikakkiyar fulani ce yajuya kenan yaji muryar ta nacewa hansai kizo mu zaga, hansai tace to bara nasha nono, Duk wannan zancen cikin harshen fulatanci suke yinsa,

Ganin suna kokarin juyowa yasa yamaza yalabe jikin wani iccen tsamiya, suna wucewa Yakoma mazunin sa, yadauko wayarsa yana daukar guraren da photo

  FULANIN DAJI
N@ B aleeyu  page 5
Se guraren la'asar suka koma gida, joda tacire kayanta tashiga aykinta wato bacci, gwaggo tashigo kawomata abunci ta ganta aleme tana bacci tace oh ni ma'u ko sai yaushe yarinyar nan zatayi hankali oho,     

Mahmud yacewa Ahmed, ni man banganeba se yaushe zamu fara training din nan yaufa kawanan mu 3 , Ahmed yakallesa se randa kasaka tym, Mahmud yace oh dama ni kake jira ne, Ahmed yace of course, batareda yadago kansa ba Mahmud yace shikenan kobe za'a fara fita aiki, Ahmed yace ok

Yauma kamar kullum Mahmud yazo shan fura zuwa yanzu har sun Dan saba sedai sun kasa sakin jikinsu dashi,sosai ,  shima dai yafahimci hakan saboda haka yashiga yin wasa dasu yana basu labarin sa,

tagama dama masa furar sa, setaga yadauko wani Farin dutse a leda tace lah miye wannan zaka saka yace kankara ce sanyi zatayi,  hava ta wangale baki tana kallo, ba afi minti ukku ba kan karar ta narke, Yace ungo shakiji yadda  tayi tuni tasadda kai kasa, murmushi Yayi to sarkin kunya, bani roba sena zuba miki,

Da sauri tace a'a kabarshi, Yace kinga koh wlh zanmiki kuka idan baki shaba,  joda tace kuka kuma Dan allah kayi hakuri wlh bazan iya shan wani abu a kasuwa ba, murmushi Yayi to shikenan na fahimceki

Kullum haka yake bata dari biyar yace tarabawa almajirai ragowar, ita kuma bata fasa zubasu aramen ba, sanin halin hansai yasa ta canza gurin zuba kudin, setabar nafarkon acan, hansai zata iya dauko Su tace zata Ci biscuit kowani abu

Gwaggo tasaka joda agaba tana fada seta gayamata inda take saka mata kudi kullum se ta batarda 55 naira  , joda kuwa se kuka take domin idan da abunda ta tsana bai wuce fada ba, gwaggo abun yakara fusata ta tadauko murfin kwano ta kwadawa, joda zaki yimun shiru kose na karyeki, atake ta hadiye kukan sanin halin gwaggo, 

Gwaggo tayi Kiran hansai ta ginarsu dasuke magana da uwar hansai, tace larai Dan allah kituromin hansai, larai tace gata tana jinki, hansai duk ta tsoro ta bcoz taji duk fadan da ake yiwa joda

Ta shigo gidan se makale take da ganinta kaga marar gaskiya, gwaggo tace zonan munafukan banza , hansai tazo tazauna kusaga joda, 

Gwaggo tace kigayamun gaskiya me joda keci da kudina kullum setace ba hamsin da biyar?
Joda ta kwance hansai tuni hansai tagane nufina tace wlh in....In...da..dama.....gwaggo takwa damata murfin itama akanta, tuni itama tasaka kuka in in me kike fada dagani bakuda gaskiya

Seda Suka gama kukansu sannan kowacce takama gabanta, joda cike da tsoro tafita talla yau kam ba fira har Suka kai bakin kasuwa, suka zauna, anan gurin suka taradda Mahmud zaune yana jiransu

Murmushi Yayi musu sannunku da zuwa kanwata, yasauke musu kayan,  oya kiyi sauri kanwata yunwa nakeji, joda takalli hansai, hansai ta kalli joda,  joda tafara in in kayi hakuri yau tin gida wani yasaye furar, yanxu babu ta sayarwa

What?  Yafada yanzu kina nufin baxan sha furar nan ba, ehh kayi hakuri,  Mahmud yace bazai yuba kota waye kice yayanki yasha ay nima kudi zan biya  , bai jira amsartaba yabude ledar yaciro dawo biyar yazuba a roba yace oya zuba mun nono ni bansan yakike ba......

Shiru Yayi ganin tana kuka, oh shiit yafada, yanzu kanwata dan na dauka shine abun kuka ungo na maida yabude ledar yazuba mata dawon yakalleta yaciro handkerchief yabata, rikewa tayi Dan batasan abunda zatayi dashiba,

Kishare hawayen ki mana, Nibansan abun zai bata miki rai ba ayda bazan dauka ba, se anjima


   FULANIN DAJI
N@ B aleeyu  page 6
Joda ta tashi dasauri tariko wandonsa, yaya Dan allah kayi hakuri wlh banso ranka yabaci ba, dagota yayi yasa hannunsa yagoge mata hawaye don't worry my 6 bana fushi kingane, daga kai tayi alamar ehh

Haka yawuce aranta bataji dadiba, har Suka bar kasuwar yau babu wanda suka yiwa dariya, habu nata mamakin yauko lfy gashi yaga ko Dan bunni bata damawa fura ba yaso ya tambaya amma sanin halinsu yasa yaja bakinsa yayi shiru

cike da zumudi takai gida tadire kwaryar ajikin gwaggo,  Gwaggo tace daganin kina saurin bani kudin kinsan kinyi abun kirki wato dama dagan gan kike batarwa, joda dai ba tace komai ba se yar dariyar da take

Joda! Joda! Joda! gwaggo tace wai lafiyar joda kuwa Bara naduba, Koda tasameta adaki, Dunkule cikin bargo tana rawar dari,  subhanallah joda bakida lfy ne?  Tana kai hannunta ajikin joda tamaza ta dauke saboda zafin data jiya

Dagota tayi tana joda meke damunki sneezing dinda tafara yi da Tari yasa gwaggo yin shiru har tagama gwaggo tace sannu koh dkyar ta iya daga kanta, gwaggo tace inazuwa tashimfidar da ita tayi

Dakin baffa tashiga tadauko danyar citta da yaji da kaninfari se lipton irin nasu na fulanin daji, dama akwai wuta tadora tukunya ta aza mata, suna yin boiling tasauke suka Dan sha iska sannan ta juye a karamin cup takai mata

Ungo joda shanye kibani cup, joda cike da haushi ta shanye ganyen, gwaggo tace yauwa, sora alhini kiyi tadauko wani abu kamar tiger tazuba acikin boket da ruwan zafi, ta kwabe wa joda kayanta daga ita se pant

Blanket tasaka tarufeta dashi hayakin dayajin suka dinga ratsa ta har ruwan yahuce sannan gwggaggo tadauko mata wasu kayan tasaka mata  tarufe ta da bargo, taje tadauko kasko da garwashi aciki ta ajiye mata gefe inda tasan bazata shure ba,

Hansai tazo biyawa joda suje talla , gwggaggo ta sanadda ita joda ba lfy, tace gwaggo meke damunta, gwaggo tace yo hansai ai ta tsuniyar gizo bata wuce ta koki, hansai tace oh ni husainatu ko se yaushe wannan shegiyar murar zata sakemun yar uwa,

Gwaggo tace mura kam ai sedai ta mutu da ita Dan tagado ce tin kaka da kakani ansan fulani da mura balantana ma mu damuke fulanin daji, hansai tace to kenan yau bazuwa talla koh?

Gwaggo tace aikodai babu,  hansai tace a'a gwaggo yanzu yadda za'ayi ki kawo dawon se nasamu yaro  basa nera goma  yakai mun kasuwa, gwaggo tace ba ayi haka ba ya zakiyi da sana'a biyu wazai dama miki furar wazai sayadda shinkafar, hansai tace to ai zuba shinkafa ba wuya , kawai ki kawo gwaggo bazan bari kiyi asara ba, Duk yadda gwaggo taso tabar shi amma firrr hansai tace   zancen ba , dole gwaggo tabata dawon

A runfar mai shayi tayada zango, habu yace hansai lfy yau ina yar fillo, hansai tace wlh batajin dadi ne, habu yace ayya ki gaida ita Dan allah ba komai zataji

Mahmud yazo yazauna tareda sallamar shi, hansai takarba seda yayi Jim kadan sannan ya tambaya , cewa ko ina joda yau, hansai tace batajin dadi ne , meke damunta Mahmud ya tanbaya? Hansai tace mura ce , ayya kozaki kaini gidanku in dubata, Mey? Hansai ta tanbaya, Mahmud yace cewa nayi ki kaini gidanku in dubata,

Hansai tace kayi hakuri wlh za'a mun fada, Mahmud yace fadan me kuma? Hansai tace kaga mufa ko makwabcin mu ba abari muyi fira dashi, Mahmud yace to nifira nace zanyi dake gidanku nace ki kaini induba yar uwarki

Hansai tace naji babana zaice a ina nasanka kuma ya hanani kula maza sena girma,  dafe kansa Yayi ganin yayi gabas tayi yamma, Duk yadda yaso ta fahimta takasa hakan yasa yakyaleta, badan yasoba yau ko furar bai sha ba yayi wucewarsa.........

Muje zuwa 
ASEEYAH BASHEER ALEEYU
9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: FULANIN DAJI
N@ B aleeyu  page 7
Kwanan joda 3 tana famada zazzbin mura, hansai kuwa tacigaba da fita da fura,  haka Mahmud yake zuwa gurin kullum  Yayi mita har yagaji akan hansai takaishi gidansu joda amma taki dole yahakura

Joda an warware yau tafito tallah duk tarame se laudi take kamar taliya, dama can haka take kamar zata karye, tafe suke suna firar  yadda hansai ke gudanarda sana'arta  biyu lokaci guda fura da shinkafa kenan,

Hansai tace ke bafa  wani wahala , joda tace nagode hansai allah yasaka miki, hansai tace kinyi fa haramun, joda tace menayi kuma na haram? Hansai tace godiyarki mana, joda tace to Dan nayi miki godiya shine haram, hansai tace sosaima kuwa yaushe zaki godemun akan abunda yake wajibi akaina , idan  banmiki wazai miki, Miye amfanin abotar mu idan ban taimaka miki ba musamman wannan lokacin dakikafi bukatar taimakon,

Joda tace hakika ke qawa ta gari ce, ba kowace kawa zata gane hakan ba , allah yarbamu tare ameen yarabbi,

Mahmud yayi tagumi yana kallan joda, kanwata kinrame dayawa fa,  murmushi tayi tasadda kai kasa, to sarkin kunya zaki fara koh, hansai tace aifa inaga wannan kunyar tata ita zata bata wahala nan gaba, dariya Mahmud yadinga yi, yana mamakin irin yadda suke zance kamar wasu manya,  yaran dabasu wuce 13  years ba,

Yau kam yasha fura kusan ta dari, sannan aka dama masa wata yatafi da ita, hansai tacewa joda, joda inagafa Mutumin nan bashida aibu , saboda haka mukaima gwaggo kudin nan inba hakaba wlh zata kidemu tamkar ganga, joda tace so kike gwaggon tawa ta bace ai wlh gwara tadakeni data bace kinaga Yan bunni da akace basa cin abuncin irin namu, amma shi wannan kullum seyasha furata, kofa shi babu

Hansai tace to wlh baruwana idan gwaggo ta dakeki ni zance bansaniba kona gayamata gaskiya, joda tace kada kimun haka hansai, hansai bata saurareta ba tayi wucewarta

Joda kuwa nazuwa gida ta ajiye kwaryar bakin kofar dakin gwaggo tasaka kudin aciki, tashige dakinta tana kuka sanin hukuncin ta, gwaggo nafitowa dakinta taci karo da kwarya bismillahi shine abunda tafada, joda! joda! Tashiga kwala mata kira, lfy kika ajiye mun kwarya a kofa kadan takadani, mtsss yanzu haka fitsari yakorota shine tayadda kwaryar anan

Adakinta tasameta ke bani ragowar kudin in baki ki auno mana dawa yau tuwo zamuyi dumm dumm taji gabanta yafadi , a rude tace gwaggo wlh muna gudu suka zube ahanya, gwaggo tace Mey? Wlh karya kike kwanan hansai ukku tana fita da furar nan amma bata taba batarda ko sisi ba seke koh, wlh yau kasheki zanyi, jin zancen gwaggo kuma tasan halinta zata iya zaneta tsab, yasa  tafara kuka da karfi, gwaggo kuwa tafita neman bulala

Jin kukan joda yasa hansai fita aguje har tana tuntube , tana isa tafara Kiran gwaggo gwaggo tsaya nafada miki gaskiya, gwaggo tace oh dama kunsan abunda kukeyi dasu kenan, Hansai tace wlh gwaggo bakashewa muke, gwaggo tace to uwarme kuke Ci dasu, Nan hansai ta warware wa gwaggo komai

Gwaggo kam ta tsorata ainun tace aiko in haka ne kin dena tallar gabadai, bazan yarda kije ya salwantar mun dakeba, joda tafito daga daki tarungume gwaggo tana kuka, gwaggo tace kiyi hakuri yata ai dakin gayamun bazan dakeki tun farko ba, kiyi hakuri kinji bamazaki sake zuwa ba kinji koh, tagyada kai, hansai tace dajin ja a dakeki abanza se tsoron duka amma ba.....bata karasaba joda ta jefamata Dan kwalinta, to kinfada kinji dadi

  FULANIN DAJI
N@ B aleeyu page 8
Sanin tanbaya da Mahmud zai mata yasa tacanza gurin zama dukda cike take da kewar joda,

Mahmud kuwa yazo gurin yayi taji ra yaji shiru gashi yau habu mai shayi bai fito ba, dole yahakura Yakoma gida cike da takaici ga yunwar dake da munsa

Joda sundawo daga makarantar allo tana rike da allonta da sauran littattafan ta, hansai tace joda Dan allah mubiya kogin kada muga wasar alkuku, joda Ta ware ido Mey?  Wlh kyaje ke kadai nikam ba inda zanje kada yacinyeni, hansai tabata fuska kefa shegen tsoro ne dake daga kallo mezai kaimu aciki ne, Kinga tafiyata inbaki zuwa,

Joda ganin ran kawarta yabaci yasa tace to muje nidai amma wlh bazamu dadeba kinsan yau baffa na gida, hansai tawa she baki ai bazamu dade ba yanzu zamu dawo

Suna isa bakin kogin suka samu gefe guda saman dutse suka rakube suna kallan wasa, joda se juye juye take, ita duk tsoro takeji ga gurin da shegen sanyi , ita bawani kayan kirki tasaka ba, kayan fulani ne ajikinta ko mayafi babu tini tafara rawar dari, Nan danan tafara sneez, takalli hansai taga ita ko ajikinta, tace hansai mubar nan gurin allah gabana kefaduwa kuma kinga munyi nesa da masu wasar nan kada majici yazo, hansai tace aike illata dake shegen tsoron tsiya ne dake wlh, joda tace nidai natafi sanyi nakeji,

Dole hansai ta tashi tabita suka bi hanya koda suka zaga maza suncika gurin,  dole suka koma bin hanyar baya inda babu taron mutane tafe suke joda na rawar dari hakoranta se bugun juna suke,

Hansai ce gaba joda baya, Wata hanya suka bullah mai shegen duwatsu manya2 dasu, hansai tace lah kinga joda daga munbi can se dajin damuke kiyo, aiko ma wannan tafi sauri wlh,  joda dai ba tace komai ba se biyar ta take, can taji ta taka tasaya tace hansai na taka kaya fa zoki cire mun, hansai tazo tace kai yabakiyi kuka ba kayar babba cefa kuma ta shugeki , joda tayi tsaki dallah kici remun in zaki iya

Hansai taja dakarfi , Wata guguwa ta taso gurin kura tacika musu ido iska yadauki hansai sekan dutse kanta yabugu, joda kuwa mulmula tadinga yi hartakai gab da wani icce tarike shi gam tana,  wayyo allah na kutaimakeni, hansai kuwa tana tasaki tasaka kuka dab bataga joda ba, can tadinga jin ihunta, dasauri taleka taga joda gab da ruwa ga kada can a gefe se bude baki take, tuni itama tasaka ihu

Ahmed dake gefen ruwan yana kallan Su duk haushi yacika shi, to inba iskanci ba meyakawo mata a kogin gurin da maza ke zuwa, abun haushi ma yadda suka cika gurin da ihu , karar da aka saki sakice yadawo dashi daga tunanin dayake dubawa da zaiyi ne yaga har tafada ruwan itakuma waccan mahaukaciyar se hauka take, acewarsa itakuma hansai ganin kada tayo kan joda babu ko tantama cinyeta zatayi

Dogon Tsaki  yaja ganin irin ihun dasuke domin idan da abunda ya tsana baiwuce hayaniya ba musamman ma na mace ,kai mata jakai ne wlh mtssss , , , ,  nikuma asea  nace harda uwarka

Gun naga yajanyo a aljihun rigarsa , yasaita dai2 kadar yahalba toni gurin yadau wani irin ruri nikaina seda na tsorata irin yadda kadar ke fitar da iska tareda wani ruri kamar ana kidan ganga sekuma ta tarwatse lokaci guda

Jacket dinshi yacire, yafada ruwan kai lallai Ahmed ya iya ruwa nibanma gansa ba yanutse a ruwan se can nahangosa yadauko joda tamkar gawa, sekuma yasake nutsewa, nemansa nake wai sai gashi agabana har yafito rungume da ita fuskarta acikin kirjinsa duk ta dungule da alama tasuma dakyar ya ban bareta ajikinsa duk ta San kare  tsaki yasaki ganin duk tabata masa farar riga da shegen Jan bakin ta  jacket dinshi yadauko yasaka mata

yajuya zai wuce kenan yaji kamar anrike masa hannu juyowar da zaiyi yaga ashe sarkar dake kan kunkurunta ce tasarkeshi janta yayi dakarki base gata tawatse ba , haushi duk yakama shi yawuce yadauko wayarsa da glass dinsa yawuce abunsa

Hansai taleka taga yabace tafito dagudu tazaga ya gurin da ya ajiye joda, ta aza kunneta kan cikinta taji tana Dan sheda kadan2, Alhamdulillah tace,  sekuma ta tashi dagudu bata tsaya ko inaba se bakin kasuwa ta taro mai jaki , suka aza joda saman jakin suka yi gida da ita,

Suna isa kofar gidan tace ma jakin yashiga,  gwaggo na surfen dawa taji kamar takun dabba dagowar dazatayi ne taga joda ajikin jaki, ai batasan randa tasaki tabarya ba tana subhanallah lfy hansai meya sameta,  hansai tace gwaggo sauketa  ,



gwaggo tasauketa takai ta daki hansai tace gwaggo bani nera ashirin in bashi , gwaggo ta kwance zaninta tabata, hansai tamika masa yayi godiya yawuce.......

  FULANIN DAJI
N@ B aleeyu  9 page
Gwaggo tace hansai nifa banganeba meya sameta ne dubi yanda naganta duk gashin jikinta atashe gashi gabanta se faduwa yake kamar ma a some take, meyasameta naga jikinta duk ruwa ne kasan kafarta jini ??????

Hansai tafashe da kuka gwaggo tajanyota har tayi shiru sannan tagaya ma gwaggo abunda yafaru, takara dacewa ni dama ina tsoron wannan yaron Mahmud daganinsa bayahude ne, gwaggo kinga yadda yabidda bunduga  (bindina) ya kashe kadar nan kwarankwatsa idan kikaji yanda tayi wani gurnani, gwaggo tace aikuwa duk dajin nan ba inda ba'aji ba,

Hansai tace kinsanme gwaggo wlh yanda yayi tsallen kwado yafada ruwa shike bani mamaki nutsewa fa yake a cikin ruwan tamkar kifi , gwaggo tasa dariya, tace nidai allah Yayi muku tsari da wannan bayahuden yaron  ameen

Gwaggo tacanza ma  joda tufafi ta hada mata ruwan wanka tareda ganyayyaki aciki tagasata sosai sannan kuma ta saka garwashi adakin, hansai taki komawa gida gefen kadon karan joda tazauna tana ta addua allah yasa kar murar joda ta tashi,

Joda ta warware sedai yar mura dake damunta gakuma yawan firgita datake yi data kwanta seta tuno wannan Ahmed din bakomai take tunawa ba irin yadda Yayi tsalle kamar aljani yanzu ko zata rufe idonta idan taga hakan

Hansai kam tadena fita tallah acewarta tsoron take tahadu da makashin nan, Mahmud yayi sintiri har yagaji baigansu ba, dole yahakura, Gashi sunkusa komawa tinda dama 2weeks ne zasuyi yanzu sunyi kwana goma

Ahmed kuwa yana zuwa gida yacire kayan jikinsa ya shanya Su  wanka yasake yi yafi awa yana darzar jikinsa acewarsa yatabi najasa, domin kauyawa nazajasa ne agurinsa musamman ma wadannan na daji gwanda kauyawa da Su,

Mahmud dai yagaji da sintirin gurin yatanbayi mai shayi koya San gidan Su joda, mai shayi yayo masa kwtancen dukda baiganeba yace yagode, yabi hanyar gidan yana tanbaya abun mamaki duk Wanda ya hadu dashi se yaga suna guduwa, shi azatonsa duk kauyancinne

Nanko baisan kayan dake jikinsa suke tsoro ba, wato soldiers uniform dinshi, dayake ma farar riga yasaka wandon ne kadai na soldiers  se hula,  hansai yahango, wani farinciki yaji ya lullubesa yakarasa kanta yana cemata to gani a gidanku ay gidanku ba zaiyi wuyar ganewa ba tinda duka dajin nan ba kuyi 5 hundred ba,

Hansai tace Dan allah kada ka kasheni wlh banmaka komai ba, Shiru Yayi yana kallanta da mamaki in kasheki mekika yimun ko ance muki ni makashi ne,

Hansai tace nidai Dan allah kada harbeni kamar yanda ka harbi kadar nan ajiya, Mahmud yace wai mafarki kike kome kinga inane gidansu joda , tace wlh baxan nuna maba ka kasheta ay nasan ji yama ita kaso kashewa seka harbi kada wato kaga munki cin kudinka mubace koh mugu kawai

Ana haka Sega baffa yadawo dauke da kara yace hansai lfy naga kinyi narai2 da ido, ta nuna masa Mahmud, atake yace innalillahi wa inna ilaihir rajiun, yaro lfy meya kawo mana makashi anan

Mahmud ya mai mata makashi kuma?  Se alokacin yatuna kayan dake jikinsa, Yace I'm so sorry dady, baffa yace ce maka akayi munajin wannan yaren naku na ya hudu da nasara,

Mahmud yasosa kai yi hakuri baba, yanzu duk ba wannan ba naxo duba joda ne inji ko lfy kwana biyu nadena ganinta kasuwa, baffa yace ai kafi kowa sanin halinda take ciki kazo kuma yanzu kana tanbayar mu,

Kaga mungode da taimakon da kayi mata Dan girman allah kayi tafi yarka, muba muyi yi muku komai ba kinzo kina wani zanse can nadaban, se a lokacin Mahmud yalura da yadda suke duminsu, abun ma seya bashi dariya

Ganin yadda Mahmud ke dariya yasa baba yin maza yasaka hansai cikin gidan yarufe ganbun........

Muje zuwa
ASEEYAH BASHEER ALEEYU
9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
     馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
        馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
          馃巹 馃巹 馃巹
              馃巹 馃巹
                 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�
Ahmed mura yakama shi sosai har ba'a jin zancen sa, sneez yake tamkar bunsuru 馃槀 , ga zazzabi yarufesa sosai, aransa kuwa allah ya isa ya keyiwa joda shegiyar bafulatana, natabbatarda sneez dinda take ne lokacin dana daukota aruwa shine ya shafeni ta likamun ciyon Su shaggun fulani, kuji Ahmed to waya saka dole ne 馃槒

Mahmud yashigo dakin da sallama bai amsaba dama kuma haka halinsa yake, tsaye yayi ganinsa acikin blanket, kafada yadaga , mutun kullum a kwance tamkar ruwa tsaki yaja yayi ficewarsa,

Tea yahada mai kauri yasha tareda  cake , yagama sha yadauko system dinshi yana dubawa,  wani video yaga ana forward na wasu terro a garin bauchi , yafara Kiran Ahmed! Ahmed! Zokaga Dan allah jin shirun Yayi yawa ko motsi baiga yanayi ba, yasa shi ajiye system din, yaje ya yaye masa bargon da yayi rufa dashi, gwale idonsa yayi ganin yadda Ahmed ke rawar dari gakuma hakoransa se haduwa suke da juna bai kara rudewa ba seda yakai hannun sa kan  Ahmed yaji zafi radau gakuma jijiyoyin kansa se bugawa suke,

Subhanallah meyasameka man, Ahmed yakasa amsawa se kansa dayake nuna masa,  ga atishawar data damesa dakuma Tari , Mahmud  dafe kansa Yayi , mezanyi yanzu naji yafada, kome yatuna, naga yazubura da karfi, yadauko bag dinsu duk ya watse kayan amma baiga abunda yake ne maba,

Yanzu idan nakira gida zan tada hankalin Dadyn Ahmed da kuma kanwarsa Hafsa, to yazanyi wannan serious sick ne abunda yakai man kawance aiba karamun abu bane,

Fita yayi yabi hanyar kasuwa, har yakai cikin kasuwar ya tsaya yana tambayar ko akwai inda ake sayadda magani duk Wanda ya tanbaya dariyar sa suke, domin Su kowa shi yake yiwa kansa magani dakansa, dkyar yasamu wani tsoho yayi musa kwatancen wani gida yace nan ne a kullum baza arasa magani ba kowanne iri, Yace Dan allah baba kataimaka muje tare, bazan gane ba gidajen kamar iri daya ne,

Haka kuwa akayi tsoho yarakashi har bakin gidan, zai wuce ne Mahmud yace baba nagode amma kozaka iya mun sallama da mai gidan, tsoho yace mushiga bakomai gidan aminina ne, suka shiga da sallamar Su, gwaggo ta karba tace musu ai baffa yatafi daji , tsoho yace aidama gurinki mukazo, gurina kuma inji gwaggo? Tsoho yace ehh wannan yaron bakin dajin nan ne inaga daga bunni suke, magani yake tambaya nace bari na kawo shi nan kozai samu,

Gwaggo tadubesa da kyau tace wannan ai bayahude ne koh?  Mahmud yayi murmushi yace inna nifa musulmi ne kesan mu Yan birni munada banbanci daku, amma kudena kiranmu yahudu, yahudawa fa,  ba musulmai bane, gwaggo tasosa kai, tace to wane magani kake nema, Mahmud yace na mura da zazzabi da ciyon kai, gwaggo tayi dariya tace to ay duka ciyon guda ne murar Itake haifar da zazzabi da ciyon kai kafahimta , Mahmud yace ehh,

Gwaggo ta hura wuta dayake wutar karace nan da nan wutar ta ruru, ganyen shayi ta aza tareda citta da yaji da kaninfari , suka tafasa tajuye acikin wani kwano, inazuwa tace,  wani mai tabasa tamkar RUBB  tace wannan kashafa ajikin ka sannan a zuba acikin boketi a rufe jiki dashi hayakin da yaji nashiga jikinka insha allahu zazzbin zai karye murar kuma zata yi dama,

Mahmud yayi godiya yace to inna nawane kudin, gwaggo ta ware ido, idan akayi taimako biya ake? So kake in siyadda ladata a'a kam sam bazata sabuba, lokaci guda yaji gwaggo tashiga ranshi dama ace haka sauran jama'a suke da an rage zafin wani abun

Sunafita yadauko dari biyar yaba tsoho, tsoho yaki karba yayi2 yaki karba dole Yakoma da abunsa yaba dada godiya, yana isa gida,  yazube shayin a cup  Yadago Mahmud yabasa abaki,  Mahmud baiyi gardamaba ya shanye tass sema dadin shayin yaji saboda yanda yake da zafi gakuma yaji,  boket yadauko yazuba man, yazo yacewa Ahmed kazo ga sauran maganin kayi tiraren ruwan zafi, Ahmed yace a'a kabarshi bana iya tashi jiri nake gani

Dagosa yayi yacire masa riga da wando yabarsa daga shi se base da wando karami, Ahmed yadago ido yana kallan Mahmud yace wannan iskancin fah yazaka tubeni bayan kasan sanyi nakeji, Mahmud yayi masa banza yacigaba da abunda yake, yazuba man da ruwan zafin, sannan yakawo Su agaban Ahmed ya ajiye yazanyo bargo ya lullubesa, kusan minti goma sannan ya bude shi, idonsa alumshe, zufa se karye masa yake,

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 1鈨�1鈨�
 Saman gadon yamaidasa yasaka masa wasu kayan, ya rufe sa, nana da nan bacci, ya kwashe shi, Ajiyar zuciya Mahmud yayi yace allah yasa yatashi garau, mu Ida wannan mission din lfy,

Karfe 8 dai2 Ahmed yafarka , jikinsa garau se wani karfi daya keji, aransa yace wannan coffee din yayi energy coffee ne kenan dubi yadda nakejin karfi kamar zan iya fasa gina, lol
Mahmud yashigo dakin rike da kwanon fura ya ajiye gefe guda, Yace D boy yajikin, Ahmed yace normal wlh, coffee din yayi fah, ayki dari da dari yake, magani karfi, ga dadi again etc,

Mahmud ya kyalkyale da dariya, waya cemaka coffee ne, coffee nada yaji ne? Ahmed yace oho to shayi ne koh? Mahmud yace koma dai Menene yanxu dai your normal so baruwanka, kafada yadaga, itso k"

Mahmud yadauko furarsa yazuba kankara yafara sha , Ahmed yace wai Dan allah meyasa kai kake bala'in kazami, yanzu Dan allah furar Yan dajin nan kake sha , kofa fanfo basuda sedai ruwan rijiya, kai bakasan wanda wa yayi dawon ba komai tsabta ne koya, kilama an gurin dakansa ansaka da gwuda andake da sauro.....

Mahmud yace ya isa haka, idan bazaka shaba ka kyaleni yazaka dinga kiramun kwari acikin abunci na, sokake inyi amai, Ahmed yace allah sauwake insha wannan abun, Mahmud yace okay better keep mouth

Ahmed yace base kace ba, ni inzaka sha wannan kazantar karika shan sha acan waje Dan wlh zubadda ita zanyi kasan bana son ganin irin wannan useless din, Mahmud yace shege kafasa koyanxu zaka iya zubadda ita , Ahmed yaza tsaki yafita daga dakin, yana fita Mahmud yace kai bakasan dajin daka raina shine yayi maka maganin ciyonka ba Dan iska kawai

Joda tace Dan allah gwaggo kibari nacigaba da tallana kinga anata zuwa nema , gwaggo tace nidai hankalina baya kwanciya akan hakan wlh kinga ko hansai tadena zuwa, tace Mutumin nan makashi ne, da bundugar shi a aljihun sa

Joda tace wlh aa gwaggo bashi bane wannan mafa ya iya ruwa Mahmud kuwa yace tsoron ruwa yake , gwaggo tace kajiki da shirmen banza komai zai iya cemiki Dan yaci galaba akanki, joda tace wlh gwaggo bashi bane kamshinsu ma badaya ba,

Gwaggo tace shikenan tunda ke bakya jin magana dole joda taja bakinta tayi shiru, can kuma tace gwaggo yanxu a ina zamu sami kudin.....gwaggo tace wlh joda zan saba miki wato ni ban isa dake bakoh, joda tace gwaggo kiyi hakuri nadena zancen wlh, gwaggo tayi hanyar bayi batako bi takan joda ba

Baffa yashigo gidan jayeda saniyar sa, yaje gurin dasuke ajiye Su, yaturke ta, yazo yazauna yana Kiran ina auta joda, joda tafito da gudu baffa na, sannu da zuwa,  baffa yace ina gwaggonki, joda tace tasiga bayan gida, baffa yace  to zoki bude mun wannan ledar nakiya ce na siyo muku,  cike da zumudi take bude ledar gurin sauri har rawa hannun ta keyi takasa bude ledar, baffa yace kawo nabude muki mai kwadayi,

Gwaggo tafito daga wanka, ta yiwa baffa sannu da zuwa takawo masa fura da ruwa,  sannan taje ta shirya tazo tazauna sunata fira,  sallama sukaji anyi daga waje,  baffa yace joda jeki dubo wake sallama awaje, takalminta tasaka tafita, wazata gani lah yaya Mahmud waya nuna maka gidanmu shima dai mamaki yacika shi, yo dama nan gidanku ne, joda tace ehh mana bagasi kinganni asiki ba, Mahmud danne dariyar sa yayi domin in suna wannan zancen dariya suke bashi,  tace bismillah sigo siki, Mahmud yasaki yin sallama yashiga ciki.......

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 1鈨�2鈨�
Baffa yamike tsaye da sauri yana nuna Mahmud da yatsa ke meyakawoki gidana sanake ziya nakoraki daga hanyata , saboda allah me mukayi miki kike bibiyarmu, mufa baruwanmu daku yahudu da nasara,

Gwaggo tace dama shine kake gayamin ziya, baffa yace sine mana, ziya da kayan yahudu yake yaukuma kinga yasaka na narasa, gwaggo tace zo zauna yaro, baffa yace kuttt bilahilazim bazata zauna gidana ba, canake angaya miki makashi ne,

Gwaggo tace insha allah shine Wanda nabawa magani jiya, yaro zoka zauna , Mahmud se murmushi yake yajanyo kujera yazauna, baffa ma Yakoma yazauna, gwaggo ta dubi joda tace joda wannan shine yafidda ki ruwa,  joda tace a'a bashi bane ba wannan kamshin bane, Mahmud ya zaro ido kamshi kuma sekace dai mai wanka da tirare, gwaggo tacewa Mahmud bawan allah kagayamuna tsakanin ka da allah meyasa kake bibiyarmu

Mahmud yace bakomai atareda ni se alkhairi inna ni musulmi ne, kuma mai tsoron allah ne, wani aiki mukazo yi nan dajin jibi zamu koma gida, gwaggo tace to ai ba'anan gizo ke saka ba, kowa yasan Yan bunni da kyama musamman garemu amma kai babu wannan kome yasa? 

Mahmud yayi murmushi yace to inna miye abun kyama ga talaka ko ba kauye bayan allah dayayi mu shi yayi ku kuma badan baisonku yayi ku ahaka ba sedan yajaraba imanin , haka muma badan munbiyasa dako sisi ba yayi mu wayayyi masu kudi, badan kuma yafi kaunarmuba akan ku sedan yajaraba imanin mu yagani shin zamuyi amfani da dukiyar mu dayabamu da ilimin mu mu aiwatarda alkhairi, mukuma siye aljanna da ni'imar da allah yabamu

Baffa yanisa yace hakika wannan yarinyar tasan allah tasan abunda take zucitarta cike take da zuhudu, yaro ka gafarceni, Mahmud yayi dariya yace bakomai baba nidama burina ku yarda dani ku kuma yafemun akan sakaku danayi acikin Dar Dar nakasancewata mutum nagari,

Gwaggo tace wlh bkomaie ay muma rashin sani ne, murigada mun dauki Yan bunni abun gudu da kyama , Mahmud yace ay turawa sune ake kira da yahudu da narasa ko acikinsu akwai musulmai dayawa,

Baffa yace wani yare ne ake kira turawa kuma,  Mahmud yace a'a wani jinsi ne na Dan Adam a wani yanki ne cikin duniyar nan, baffa yace bayan kano damuke  ji sekuma birnin shehu se gombe  da sauran kauyuka kamar Su binji da sauransu akwai wasu kasashe ne,

Mahmud yace ai duk wadannan garuruwa ne kano da sokoto, Duk acikin kasa dayane Nigeria, baffa yace me cece Nigeria kuma,  Mahmud yace kasa ce duk acikinta muke sauran kasashen duniya a jirgi ake zuwa, gwaggo tace ni wlh nakasa ganewa, Mahmud yace bazaku ganeba inna  saboda da ace kuna cikin gari ba dajiba duk zaku San wannan kauyawa ma sunfiku civilizations ,

Yace ina zuwa wayarshi yafidda musu ya kunna musu baffa zai tsoro yakeji yadda yake ganin al-amurran wayar, joda kuwa se ihu take, Yace joda zonan kigani tadawo kusansa hannunsa yasa yarungomota yadau kesu photo . yanuna mata tsoro yakamata sosai, Kiran gwaggo take, gwaggo zokiga mune fah muka fito acikin wannan abun,

Haka yacigaba da daukarsu photo harda Su gwaggo da baffa yanata nuna musu suna jin dadi, Se kusan magrib yabar gidan cikinsa cike da fura,

Koda ya isa gida yatarda Ahmed rike da jarida yana karantawa, baimai sallama ba sanin halinsa, shikuwa Ahmed hakan yasosa ransa nanko yakara kimtse fuska, Mahmud Baiko kula da halin dayake cikiba, wanka yayi yatada sallah abun shi koda yagama Ahmed yafita,  saman gado yafada ya kunna wayarshi yana kallan pics dinsu, tsurawa joda ido Yayi yau batayi kwalliyar hauka ba, kamar ma ba dade da wanka ba

Fuskarta tayi haske sosai sedan kufan Jan bakin dake bakin ta ba inda take da Dan kwali ya tsurawa gashinta ido lallai wannan gashin idan yaji retouch zaiyi kyau, haka yacigaba da sake2 sa aransa har bacci yakwashe shi,

Joda takoma ma fita da farar ta, hansai ma dole takoma ga tallanta na shinkafa, Mahmud kuwa yamaida gidansu joda gurin firar sa, yayi ta shan fura baruwansa da wani kyankyami, joda kuwa tana makale dashi ya kunna mata wayarshi tagani haka zai dinga kunna mata pics tana kallo tana ihu,

Yau tin safe yatashi yahada musu kayansu tsaf Dan yasan wancan Dan iskan Ahmed  ba hadasu zaiyi ba, yagama yacewa Ahmed inazuwa bai amsaba Shikuma yayi ficewarsa sai gidansu joda,

Joda kuka take sosai tarike Mahmud,  yace mata kiyi hakuri joda zandawo nanda sati guda , tashare hawaye da gaske yaya kayi alkawari? Yace nayi joda , Gwaggo takawo galan din fura da nono tabashi Mahmud yaji dadi sosai yadinga godiya,

Kudi yaciro yabasu amma suka ki karba seda yayi kamar zaiyi kuka sannan baffa yace dari biyar ta isa badan yaso ba yamaida sauran,  har bakin kasuwa suka rakashi......

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
     馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
        馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
           馃巹 馃巹 馃巹
              馃巹 馃巹
                 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 1鈨�3鈨�
Dan achaba suka tara yafitar dasu daga dajin dama kuwa Dan achaba biyu tak adajin semai kudi ke hawansa bayan Yan keken mai garinsu wato wanda yake babba adajin yanada keke biyar wadanda ake masa haya dasu
Wannan kenan "

Tafiya sukayi mai nisan gaske tun Karfe tara nasafe suke tafiya adajin basufita adajin ba sekusan 12  waima saboda suna gudu,  dari biyu2 suka biya sannan suka sake taron wani Dan achaba yakai Su cikin gari nanma sunyi tafiya ta kusan 1hr sannan suka isa cikin gari,  anan naga sun tsaya Mahmud yakira a turo musu mota takaisu airport,

ba afi 20mnt ba segasu mota kusan ukku tareda soldiers 6 kowane dakayansa Saye kowace mota soldiers biyu ce aciki tagaba ita aka saka bag dinsu, tabiyu Ahmed yashiga dayan soldier yashiga gaba se maijansu, ta ukkun itace wadda Mahmud yashiga basu tsaya ko inaba se Filin jirgin sokoto,

Nan ma cike yake da soldiers sunyi layi2 kamar masu assembly, suna isa kowacce mota da mai bude ta, soldiers biyu suka musu iso suka shiga jirgi, zamansu keda wuya, aka kawo musu fish kebabs & pasta, se green smoothies,

Mahmud yaci abunsa Ahmed kuwa cewa Yayi ajaye masa shi Dan zai sashi amai, baturen yace me za'a kawo sir cikin harshen turanci, seda yadau few minutes sannan yace fish stew, Mahmud yaja tsaki yace inba iskanci ba meya banbanta wancan da wannan,  Ahmed yagalla masa harara ai dai sekaci abunda kake so koh kabarni inci wanda nakeso, Mahmud yace dayake nan gidanku be ay dole kayi yanda kaga dama mtsss yasake Jan wani tsaki

Karfe 2 daidai suka isa abuja , kafin agama tanbadodinsu inji Ahmed 馃槀 har 3 tayi dole aka hanasu wucewa gida, wani gidan aka je dasu akwai komai na bukata aciki wanka sukayi suka tada sallah azahar da la'asar, mai aiki takawo musu abunci ta lemuka ferfesun kaji ne dakuma jellop rice , kadan suka Ci, suka barshi news suka buda suna kallo, Nan Mahmud yaga wani minister yana jawabin cewa za'a tada fulanin dajin wajaki, domin bincike yanuna cewa akwai man fetur sosai akasan kogin dajin bayan nan, akwai computer tana nuna cewa akwai zinare da gold awani gida, Carab idonsa yafada kan gidan da ake nunawa akwai gold da zinare aciki bakowa ne gida bane illah gidansu joda

Tini hawaye suka wanke fuskarshi yanzu idan antada Su ina zasuje, Wadanda basu yarda da kowa ba, shiru Yayi jin minister nafadan za'a basu million guda kudin gidansu da kudin barin gari inda za'a bawa kowane mai gida dubu dari ukku da hamsin, 

Mahmud yace Ahmed dajin damuke fito ne fah, Ahmed yace ehh nagani, Mahmud yace amma kasan ba'a yi adalci ba koh? Ahmed yace sosaima kuwa yaza'a tada Su ba'a tanadar musu gurin zama ba mutanen dake tsoron birni kosunzo cikin gari wlh tsoro da wauta irin ta fulani zata wahalar dasu

Mahmud yace bama shiba, dubi wannan wake ken gidan ace 1 million kuma wai har kudin barin gari ay wannan gidan koba komai aciki filinsa kadai zaiyi 4 millions balantana akwai dukiya akasansa then kuma ace har kudin barin gidan hava it's not fair , Ahmed yace  kozaka bi musu hakkin Su ne, Mahmud yace I  think so, Ahmed yakallesa kasan kuwa waye wannan minister din, Mahmud yace koma waye shi bai isa ay shege ke maganin shege,

Ahmed yace what is it to do with them?  ar u Dsame cousin? Mahmud yayi murmushi yace se yanzu nagane baka San aykin kaba , kasata fa nake yiwa aiki base Dan uwana ba, Ahmed yace ni kake gayawa bansan aykina ba , Mahmud yace kwarai da gaske indai har bazaka iya ceton wanda baka saniba ko wanda kake kyama to lallai baka San aykinka ba

Ahmed yafusata ainun, yadauko wayarsa yace look.....sekuma yafasa , Mahmud yace mezan gani, manta kawai inji Ahmed,  haka Suka cigaba da argument har 4 tayi Ahmed yace nifa nagaji dazama nan gidan, kawai mutun yadawo dan iskanci baza'a barshi yaje gida ba , Mahmud yace kana iya tafiya ai,

Ahmed yajanyo wayarshi yakira driver dinshi yayi masa kwatancen gidan yace yazo maza2 yadaukeshi nan da nan kuwa Segashi,  amma me mai gadin gidan yaha nashi shigowa yakira Ahmed yagaya masa Ahmed yace what nonsense gidan ubansa ne koya, Mahmud yace lfy sarkin masifaffu, Ahmed yace wancan banzar mai gadi ne wai driver bazai shigo ba, sekace gidan ubansa ne

Mahmud yadafasa calm down man, order aka basa nasan commissioner ne, kasan yanaji damu soyake muhuta sosai sannan akaimu gida, duk Wanda yafito daga wancan dajin ai dole yana bukatar dogon hutu,  Ahmed yace to cemasa akayi muna bukatar hutun nibana son haka wlh, Mahmud tashi yayi yadauko masa eviron drink, ya zuba a cup yabasa, Ahmed yakarba yafara sha seda ya shanye ta tass sannan yabasa cup huhhhhhh naji yahuro iska tareda ajiyar zuciya, are you Okey Mahmud ya tambaya, Ahmed dakansa yake kasa yace yeah.......

馃巹  FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 1鈨�4鈨�
Bayan magrib commissioner yaturo musu da mota biyu kowacce akwai 2 soldiers aciki dayan tadauki Ahmed dayan kuma Mahmud kowannensu akayi dashi gidansu,

 
Wani katon gida naga an faka da Ahmed kamar wani gari, tsarinsa kadai yakoda ni , carpet ce ja mai matukar laushi ashinfide mai tsawon gaske har zuwa wata karuwar kofa kamar dai get , flowers ce shimfide ako ina, kamshi kadai ketashi narasa ta inda yake fitowa

Wata chocolate din yarinya naga tafito dagudu sanye cikin doguwar riga ta wani mayen less white & black tayi  daurin dan kwali oll back simple make up tayi amma tahadu, hannunta rike da flower  murmushi kawai take hakoranta tass dayan haurenta sanye da hauren makka

Flower tamika masa tareda rungumesa tana wlcm bros, dariya yake nikam nayi mamakin ganin wannan hero yana dariya , hw ar u 6ter?  Yarinyar tace am ok bros yagajiya, Yace bagajiya, 6ter gajiya tabi jiki shin ma wai kintaba ganin soja yagaji, yarinyar tace Au haka nefa, rugumeta yayi suka shiga daga ciki ,

Katuwar kofar aka bude zokuga wani hadadden parlour tsayawa nuna irin haduwar gurin kauyancine, ku kissima aranku kawai, Wata kyakkyawar mata naga tafito tareda wata beauty se murmushi suke, matar takarso tace wlcm son, kansa kawai yadaga mata, yarinyar tasauko daga downstairs tana wani yauki tamkar miyar kubewa  , ahankali ta furta big bros wlcm, tancuu shine abunda yafada

Yarinyar dake makale ajikinsa tace bros muje inrakaka dakinka nasan kana bukatar hutu, Ahmed yace 6ter jeki huta mana, tace no bros 2dy its ur dy, murmushi Yayi to naji muje , hannunsa tasaka ahamatanta tajashi suka bi wata hanya,  wani hadadden daki naga sun shiga,  aiko nace baza'a barni abaya ba atare muka shiga,  daki ne kato yafi hall din Dan fodio set din kujeru biyu ne aciki sannan wani wakeken gado mai runfa gadon tamkar na cikin joder akbar, kamshi ketashi kota ina , shkar kamshin yayi tareda Jan hancinsa yace 6tor I lyk it,  yarinyar tace to ay gashinan sekayita  shaka

Hannunta yajanyo suka zauna kan gado yace Hafsa gayamun dame2 yafaru bayan tafiyata me akayi miki waya bata miki rai bayan tafiyata ???? Dariya ta aza kai yaya koma me akayi ai yawuce balantana ma ba abunda yafaru,  Ahmed yace u ar lie,  nasan dole Anyi wani bazaki gayamun bane, tace yaya believe  me i swear, kafada yadaga any where zanduba camera ta, ido tagwale kai yaya allah bayasan tada fitina,

Ahmed Yace zan mareki wlh get out b4 I show you my anger ,  kafadarshi tadafa tace relax bros, tarike kafadunsa lok at me, lok into my eyes, jajayen idonsa yadago yakalleta sekuma yamaza yajanye murmushi tayi,  ta tashi tabude fridge tadauko masa eviron drink tabasa,  amsawa yayi yasha,  tace ar u okay, yeah ya amsa mata, tace gud nyt ta fice daga dakin,

Tana fita tasame wannan yarinyar da matar adakin wato hajiya da amina, hjy takalli amina tace kalleta wai ita mai yaya,  amina tace barta black gul kawai yarinya kamar yar tsintuwa babu inda tadauko abbanmu, hjy tace wayasani to ko yarsa tinda kowa yasan halin gyatumarsu, tuni hawaye suka wanke fuskar Hafsa, kofar dasukaji anbude dakarfi ce yasasu juyowa azatonsu Ahmed ne har hantar cikin Su takada, abdallah ne yashigo se tangadi yake alamar yabugu,

Hafsa tadubesa ta karkada kai cike da takaici, tawuce dakinta tabarsu atsaye, mamma zoki kaini dakina shine abunda yake fada, tace wato ba sallama kawai in kaika dakinka, amina tace hava mama baki ganin yanayinsa ne

Yace mamma yanaga anyiwa gidannan decoration ne baki mukayi, amina tace big bros ne yadawo,  Yace wht nonsense big bros dady ne, ni lokacin da zandawo daga india ba shegen dayayi mun wannan decoration din se shi mai sati biyu kacal, in possible" yadauki cup shuri yatashi sama carab se hannun Ahmed yacabe cup din dukansu suka juyo suna kallansa

Gurinsa yadum faro kamar wani zaki tafiya yake tamkar ruhit acikin doom sumar kansa nata tashi sama dukansu sun tsorata daganin yanayinsa, wuyan abdallah yacabko ya wazga masa mari,  ar u mad?  Hjy tace kai mezaka masa ne haka, Ahmed yajuyo dakarfi yana cizon lebensa, Yace dukansa zanyi zaki rama masa ne ? Amina tace bros tomeyamaka ne?

Ahmed yasaki wuyan abdallah yacakumi wuyan amina yace mekika ce, ta marmasa ido, tuni yawan ke ta da mari yadago fuskarta yasake marinta ya hankadata kasa hannunsa yadago zai sake kaimata duka, abdallah yarikesa tabaya, yajuyo yana yinayiwa hannun sa kallan wulakanci yace ina tausayin wannan kucakin hannun naka alokacin dazan cire shi anawa , hhhhh馃槀 abdallah yace wai mekake takama dashi indan Dan wannan Dan iskan cos naka wlh bazai tsorata niba............

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page1鈨�5鈨�
Ahmed yayi murmushi tareda kimtse fuska yasa hannunsa yadinga janye hannun abdallah se kat2 kakeji tuni abdallah ya kwarma ihu, Ahmed yace no no tin yanxu ya ciyo kwalarshi har sunajin bugawar zuciyoyinsu, Yace wato baka dena shaye2 ba koh? Abdallah yace meye matsalarka aciki

Hjy tace shi nagani inaruwanka da rayuwar shi, Ahmed yatura abdallah dakarfi yakaraso gurin hjy kamar zai hau kanta yace bakida hurumin hanani hukunta Dan uwana, hjy da tsoro tayi shiru gudun yamata wani abu

Tin safe Hafsa ta tashi tahada masa special break nuggets da tea se aresh da kwai , takai masa dakinsa danshi baya cin abunci a dining se in dady yana gari , ita ke basa tea din da nuggets har yagama tasaka tissue tagoge masa baki sannan itama taci nata , tagyara masa daki dukda bakomai yayi ba, tawanke toilet, sannan ta kunna bona tarufe dakin,

Ahmed yashirya cikin kananan kaya riga da wando black n Wight yaja motarshi se gidan commissioner yasanarda shi dalilin zuwansa gidan, wato yanaso acanza zancen tada fulanin daji, commissioner yace sedai kayi hakuri son amma har nacika file din , Ahmed yace  shiit yanzu miye abun yi sir gsky Anci hakkinsu akwai wani gida danagani ance wai 1 million za'a basu alhalin gidan yakai 4 sannan duk sauran mutanen dajin wai dubu dari ukku za'a basu da hamsin,

Commissioner yace karya ne masu gidan 10 million mukayi za'a basu sauran jama'ar dajin kuwa 1 million ne, Ahmed yace bahaka yafada ba a news jiya, commissioner yadauko wayarshi yakira minister, minister yace bincike yanuna babu komai agidan ansamu mistake ne afarko, girman gidan yasaka za'a basu 1 million

Commissioner ya ajiye wayar yace wannan shine fist work da zan baka kaje kabinciko mun, gaskiyar al amari, Ahmed yace ok sir gobe zakaji komai,  commissioner yayi murmushi yace am proud of you son, I sure will do it, Ahmed yace yeah sir I shall do it with my heart, murmushi Yayi yace I know son, all d best.

Haka yabaro gidan commissioner yanata nazarin yadda zai bullowa lamarin , Mahmud kuwa yanacan yana nasa tsarin, duk arude yake damuwarshi daya baisan inda zai sake haduwa da joda ba idan sukabar dajin

A DAJI KUWA,,,""
Mutanen dajin labari yazomusu cewa za'a zo atada Su saboda haka Suka fara koke2 gabaki daya dajin yazama tsit kowa da bukin zuciyarshi, gwaggo tacewa baffa tun ba azo aka wulakantasuba Su tattara inasu2 subar dajin kunsan fulani da shegiyar zuciya ,

Haka Suka tattare duk wani abun amfaninsu, gwaggo tace sokoto zasuje sunemi Yan uwansu akwai kanwar babarta dake aure sokoto amma asaninta a masina suke, dajin kowa yafito yanata kukan rabuwa dasu hansai tarike joda sunata kuka kamar wadanda sakon mutuwa yariska har sunkai bakin kasuwa joda tace gwaggo ina zuwa, ta falfala da gudu , gwaggo na Kiran ina zaki amma ina har tabace musu dole suka tsaya jiranta

Joda kuwa ramenta datakesa kudin da Mahmud kebata taje tabude tagansu kuwa suna nan, tayi hamdala tadauko har zata duba nafarko tace kai nama San hansai zata iya budewa, Dunkule Su tayi a zaninta takoma gun Su baffa

gwaggo tace mekika tusa azanin nakine haka, tace gwaggo kudin da yaya Mahmud kebani ne dik yasha fura nikuma se in sakasu arame gwaggo tace mugani, Koda aka kirga dubu ukku cib duk Yan dari biyar ne, gwaggo tace hamdan khasiran, wadannan sun ishemu rayuwar mu ko jirgi mukeso zamu samu,  lol kuji gwaggo fah馃槄

Dan achaba biyu suka tara daya da kayansu tareda baffa daya kuma gwaggo da joda, har Suka kai wajaki kauyen sokoto, Nan Suka dinga tanbayar gidan margayi alpha nuhu, dakyar suka sami wanda yasan shi yace musu ay yadade da rasuwa sedai yayan shi suma kuma ukku daga cikinsu suka rasu sora biyu mujittaba se muktar mujittaba yana cikin garin sokoto muktar na masina shida iyalanshi,

Mutimin yayi musu jagora suka shiga motar sokoto dari hudu da hamsin aka kaisu wato dari da hamsin2 abakin tasha aka ajiyesu, suka tan bayi gidan mujittaba aka nuna musu kusaga masallacin shehu inda makarantar almajiran fulani,

gwaggo cike da murna tashiga gidan kasancewar gidan da tasha titi ne kadai yaraba Su, rike take da hannun joda baffa na janye da kayansu.......
WAYE JODA?
MENENE ASALINTA?
 kubiyoni Dan jin wadannan amsoshin

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
   馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
     馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
         馃巹 馃巹 馃巹
            馃巹 馃巹
               馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 1鈨�6鈨�
Asalin joda =
Alpha nuhu shine kakan gwaggo wanda yahaifi mahaifinta wato muktar , mujittaba, ayuba, suwaiba se kasim ayuba da kasim da suwaiba duk sun rasu, dukansu yayan halimatu sadiya ne, wato matar alpha nuhu

Sadiya asalinta yar sudan ce, wato Arab agurin karatu alpha yahadu da ita anan ya aurota, yazo da ita kasar masina takusaga, kasar saudiyya, alpha fulani ne na usuli tin kaka da kakanni, kuma makoho ne sedai akwai dinbin ilimin addini agaresa hakama yayansa sunsami karatu sosai,

Alpha yarasu yabar yayansa biyar tareda matarshi, maimuna itace mahaifiyar gwaggo wadda takasance ya tafari ga malam muktar,  se kanwarta saratu sukadai ne ga  malam muktar gwaggo ta taso cikin gata da soyy sutura babu wadda bata daurawa  muji

Ganin haka yasa A'i da yayanta ukku kishi wato luba, hadiza da abdul hadi, ganin uwayensu maza sundora ma gwaggo son duniya, hakan yasa A'i biyar bokaye tana karbar magani tanayiwa uwar gwaggo da itadin, tin ta nayi yana karyewa har allah yabata sa'a

Watarana gwaggo tafito daga makarantar allo, tana shigowa gidan A'i tace mata tashiga bayi tadauko mata buta tana tafiya A'i najanta da fira har tamanta da addua daganan aljannun da aka tura suka figeta se dajin wajaki, suka yada ita sannan suka mantar da ita gida

Agida kuwa Anyi ne manta har an gaji babu haukar da uwayenta ba suyi ba daga karshe suka sangana dalilin dayasa mahifinta komawa kasarsu kenan wato masina

Ai kuwa bokanta yatabbar mata cewa gwaggo bazata dawoba se har jikinta ko jikin danta yagamu dana dai daga cikin danginsu sannan zata dawo a hayyacinta, gwaggo kuwa abakin kogin kada aka yada ita, anan ne baffa yaganta , yadauko ta saman jakinsa yakaita gidan Su

Mahaifinsa barau shine yacigaba da kula da ita har taji sauki daga nan tazama yar gida, zuwa wani Dan lokaci barau yahadata aure da dansa wato baffa,  shekararsu kusan biyar sannan gwaggo ta haifi danta  wato sani baifi wata uku ba yarasu tasake haihuwar wani shima aka saka masa sani watansa bakwai yarasu seda tayi yaya kusan biyar suna rasuwa mata da maza dukansu bada shekara suke mutuwa

Joda ce tashida itace kuma auta dalilin dayasa ake sonta kenan
Wannan kenan "

gwaggo tayi sallama tashiga gidan, Wani dattijo tagani rike sa alkalami da allo yana rubutu ahankali abubuwa suka fara tariyo mata, dasauri tace malam!
Kansa yadago yana kallanta muryar wa nakeji kamar innata, tace nice malam,  malam yace dama kina raye,

Zama tayi tadinga basa labarin rayuwar ta har zuwa yanzu malam yakalli baffa yace angode Dan uwa allah yasaka muku da alkhairi ameen,  tace malam inna baba da innata, malam yace suna masina tun bayan rashinki da mukayi, yakasa zama kasar nan, tace saratu fa?  Seda yayi Jim sannan yace allah Yayi mata cikawa, yanzu shekara goma kenan, hawaye suka dinga zuba afuskarta

Malam yace hakuri zakiyi yanxu ina zaki masina zakije ko nan zaki zauna domin nima kwanan nan nake shirin komawa can nagaji da nanan kudina kawai nakeso Su cika,  gwaggo tace nawa ake zuwa ai munada kudi, malam yace dubu goma ne duk mutun daya

Baffa hai bahause bata iya San kudi ba, mezatayi da dubu goma hanake ko makka zasu kaini, malam yace hmm nan fa ba irin dajinku bane. ....

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 1鈨�7鈨�
Ahmed yayi duk wani bincike da zaiyi an tabbatar masa dacewa, babu komai acikin gidan, amma kuma seda yasamu ganin governor da minister yayi korafi akan gidansu, haka yadinga shige da fice seda yaga anbiyasu yadda yakamata, sannan hankalinsa ya kwanta,  yakira commissioner yashaida masa yayi murna kwarai yace Ahmed kwazonka da jajircewa na burgeni,

Mahmud labari yazomasa, amma baisan wanda ya gyara al amarin ba, yadaiji dadi sosai , Yace insha allah zanje next week in kai musu ziyara kamar yadda nayiwa kanwata al qawari wato joda"

Malam yakira gwaggo yagaya mata cewa tafiyarsu jibi ne dama bagabadai zasuba abdul hadi da matarshi nanan, gwaggo badan ranta yasoba tazauna suka wuce aka bata dakin, hasiya tazauna aciki, haka suke zaman gidan a wahalce domin kuwa hadi bashida imani ko kadan, seda tagwammace zaman daji da gida, amma koba komai taji dadin ganin danginta, joda tazama boya agidan , duk jumu'a setafita da tallana ruwa bakin masallaci, dayake nan bakowa keson fura ba akwai ta ko ina ,

Ahmed yatabbar da gaskiya ya kauda rashin",, ta ma'ana yatsaya tsayin daka aka gina ma kowanne mutun gida dai2 danasa tsarinsa dai2 talaka, gidan baffa ne kadai ba'a ginaba saboda ba asamu ganinsa ba andai killace gidan, Nan cikin kauyen sokoto wamakko kudin gidan dakomai suna hannun shamsudden wanda suke cewa deeni wato PA na minister,

Ahmed yagama komai yaje yasamu commissioner yayi masa bayanin yadda komai yakasance commissioner yayita sakawa Ahmed albarka, yana fita yace aransa allah nuna mun ranarda zan aurawa Ahmed yata sarina, murmushi Yayi allah yanuna mun wannan Ranar ameen zanyi alfahari dashi cikin zuriata idan har yakasance surikina 

Ahmed yadawo daga barrack dinsu yashigo hannunsa rike da hularsa, yana takon girma karar rawar gidan yadanna mai nuna ana bukatar ganin kowa dakowa, cikin minti biyar kowa yahallara harda abdallah da masu aikin gidan hjy da yar gold din yarta amina,

Ahmed yace kunsan cewa taraku nan gurin agabadai yana nufin akwai important issue dazakuji, so ba wani abu bane, dad zai dawo gobe at 4 to 6 pm ana bukatar gyara agidan nan da cook, yakalli husaina wadda itace shugaban masu aykin abinci yace zanbaki list din abunda ake bukatar kidafa, hjy tace amma ai....Ahmed yada mata hannu 鉁嬸煆� amma me bannemi kowa Yayi mgn ba kona bada order ne, Iye?

Yamaida kallansa ga mai gyaran gidan yace tsohuwa baki bukatar gyara ko bayani you know how to make diz house special nd cute veuryfull, ar u hear me?  Tsohuwar tace Yes sir, Ahmed yace gud,  se kai mai gadi kafi kowa rawar kan tsiya idan bakayi hankali ba kana kusaga rasa aikinka,

Ali driver katabbatar anwanke duk motors din dasuke gidannan, remain you Hafsa yanuna ta, kibiyoni ki karbi keys din dakin dad kitabbatar kin gyara shi nasan zaki iya, abdallah ka kiyaye kanka daga shaye2 nan kasan abunda yakai baba Egypt natsawon wata shidda duk matsalarku ce kaida uwarka da wannan fantimotin yanuna amina, ta haifar masa da hawan jini,

So all of you b care full  idan akayi something bad or rubbish, har nagani white my ayes wlh, rankowa a gidannan zai baci,  har yajuya zai wuce hjy tace inada magana,  Tsayawa Yayi batareda yajuyo ba, Yace bayanzu ba banda enough tym dinda zan karbi korafin ku,  dts oll yayi shigewarshi

To mekuke jira muna fukan banza kunwani tsayawa kuna kallona , tadaka musu tsawa tuni kowa yasani inda zashi , Hafsa ta kunshi dariya tabi yayanta da gudu.........

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹 N@ B aleeyu 馃挄 1鈨�8鈨�
Dakinsa tabisa yabata keys din yakara jaddadamata cewa tana shiga tarufe kofa domin baya bukatar kowane Dan iska yashiga dakin , atake zasu sace wani abu tunda dukansu sunzama gwaska , Hafsa ta kyalkyale da dariya, hava yaya yadai sata, Yace  oh to karya namusu ko sharri, Hafsa tace a'a bance ba, Yace dallah kije aykinki ko sekin gama min iyayin tsiya, har zata wuce yace look Tajuyo idan akayi sallar la'asar kizo nabaki list din girki dazamu bukata, toh kawai tace masa tafita

 A parlour tasame Su hjy se zagin Ahmed suke, Hafsa tace dubi wai iskanci mutun da gidan ubansa a hanashi shiga dakinsa, hjy tace inbanda iskanci ma wai alhj zai dawo amma se abakin dansa zanji, sannan kuma shi zai tsara mana yadda komai yakasance banida ikon shiga dakin mijina se in yana ciki bani zan tsara girkin danakeso ba wai se shashan dansa

Hafsa tayi kamar batajiba tayi hanyar dakinta,  amina tace ke zonan Hafsa tayi mata banza, abdallah yace ke Dan uwarki ba mgn ake miki ba seda tajuya sannan tace ai ba ke ne sunana ba, duk Wanda bazai kirani da sunan da ubana yarada mun ba ai seya bari

Abdallah ya taso da karfi ya zare belt zai zaneta hjy tace a'a Dan mama kada ka tabata yayanta nagida,
Da kibarshi yatabata wlh in nuna masa banbancin kashi da masa,  gabadansu suka juya suna kallan Ahmed yace wato dama dukanta ake agidan nan idan bana nan, kekuma yanuna Hafsa shegiya wawiyar banza ni uwata ba haka takeba ba wanda zai takata bata rama ba bansan ko zuciyar wa kika gado ba, dad dina bahaka yakeba,

Zuciyata ce tadauko, daga kofa sukaji wannan sautin, Ahmed yace woww abba kaine, nine ahmadu muhammadul mahi "!
Hafsa ta aza dariya kai abba duk wannan sunansa ne, Yace sosai kuwa,  kema in kina so injero miki naki dasauri tace Yes inaso, yafara hafsatu manga hafsi Hafsa, Hafsa tabata fuska wlh abba banason manga dinnan, Ahmed yace kedalla kiyi mana shiru ko gaisawa bamuyi ba kin hausa da shegen surutu,

Abba yace kabarta mana, aytafi wadanda sukayi halin ko in kula dani, Ahmed yadaka musu tsawa ku sha2 shan ina ne dazakuga ubanku ku tsaya kuna kallansa amina tace ina yini, abba afusace yace da ban yini ba zaki ganni shakiyiya kawai, yagalla wa uwarsa harara, abdallah yarusuna yace abba barka da zuwa , ya amsa ba yabo ba fallasa , hjy ta tabe baki tace yaya barka da wuni,  abba yace barka De

Mahmud yashirya tsab tun da asuba yabi jirgi se sokoto, daga nan yashiga mota zuwa wajaki, yana kai bai tsaya wata2 ba yatare Dan achaba se dajin fulani, amma me yaga ya badai anrushe dajin ko tsuntsu babu balantana Dan Adam, oh gush yadafe kai bin dajin yake da ido yadda akafara foundation agurin da alama gidan mai za ayi babba , ina zan ganta wazan tanbaya?

Haka yabaro dajin rayuwar shi ajagule , kusan 4 ya isa gida wayarshi yajanyo yakira Ahmed yagaya masa cewa akwai matsala Ahmed yace Tamefa ? Mahmud yace yanzu daga dajin fulani nake na riske har antadasu, kai intakai cemaka har ankassafa gurin

Ahmed yace hava dai,  yanzun miye abunyi, Ahmed yace shine dalilin kiranka nima bansan abunyi ba yace ni yadda naji ance za'a gina musu gidaje amma banyi zaton har antada suba kodai karya ce, Ahmed yace wannan kuma seka binciki newscaster kaga inada abunyi yanzu yakatse wayar, Mahmud baidamu da halin koinkula da Ahmed yamasa ba burinsa yaga halin dasu joda suke

WAYE AHMED?

Muje zuwa 馃巹 Dan jin wannan amsar
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
   馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
     馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
        馃巹 馃巹 馃巹
           馃巹 馃巹
              馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 1鈨�9鈨�
alhj usman shine mahaifin Ahmed da uwarsu margayiya Sarah wadda suke kira da ummah, alhj usman dane ga alhj zubairu wanda yayi tashen kudi azamaninsa yarasu yabarmusu dinbin dukiya lokacin dad na jamia inda yake karatun government, musa shine babbansu wanda suke kira da abba se dad alhj usman kenan se kanwarsu zainab wadda ke aure a kt yayanta ukku rufaida yasir se muniba, rufaida tagirma tana ss2 ayanzu,

Abba musa yanada yaya ukku anty aisha se anty nana se karaminsu jalal, dukansu sunyi aure acikin kd, jalal kuwa yana turkey gurin karatu inda yake karanta business

Awani bincike da Su dad sukace sudan anan yahadu da ummah, suka kulla soyy kafin yadawo yanemi izinin aurenta aikuwa atake akabashi saboda kirkinsa, yana zuwa gida yasanadda yayanshi musa aikuwa cike da murna, yasaka musu ranar zuwa ba adauki dogon lokaci ba akaje neman auren akasa auren wata shidda dai2 kare karatunshi kenan

Yana kammalawa koda yadawo har abba musa yahada lefe yagyra masa gidansa, alhj usman yayi matukar murna da hakan cikin sati ukku aka saka biki Anyi komai lfy amarya ta tare gidan mijinta dake unguwar maitama  ,

Zamansu suke lami lfy ko gardama bata hadasu da mijinta, haka take bin abba musa tamkar mahaifinta da matarsa,  batayi shekara daya ba tasami ciki, gidan kowa murna yake dasamun cikinta bayan shekara tajuye danta kyakkyawa tamkar Dan india

Aka sha biki sosai akasa masa muhammad shine suka maidashi Ahmed,
ummah batasake haihuwa ba , alhj imaran wato mahaifin hjy ya umurci dad daya aure yarsa tunda haihuwa ta tsayawa matarshi haka yadaure ya aure ta badan yasoba sedan kawai baya iya jayayya da shi amatsayin shi na aminin ubansa, Koda dad yazoma ummah da wannan zancen seyaga tayi murna sosai hakan yasa hankalinsa ya kwanta

Hjy ta shigo gidan cike da isa da gadara, Sam bata ganin girman ummah, haka zata yi ta yima ummah habaici dayake ummah bamai son fitina bace setayi banza da ita, amma sam ummah batadaukar raini, ga zuciya kamar me irinta fulanin usuli

Hjy tasamu ciki se murna take tana kananan zancen ummah kuwa batako bi takanta ba, ahaka har ta haifi danta na miji wato abdallah alokacin Ahmed nada 6yrs, seda abdallah yayi shekara hudu sannan tasake haihuwar amina daga nan itama haihuwar ta tsaya

Shekara daya da haihuwar amina ummah ta haifi Hafsa, har an cire ran samun haihuwar , Hafsa ta taso cikin so da kaunar yayanta Ahmed skull kadai kerabata dashi,
Ummah tarasu tabar Hafsa nada shekara biyar aduniya, baqaramun tabuwa dad yayi rashin ummah ba sedai yabarwa mai duka komai

Ahmed yataso tun yana yaro da shegen girman kan tsiya, ga miskilanci har na tsiya, uwa uba bamai hanashi kudurinsa abunda kedamun mahaifiyarsa kenan, yana kare skull yaje Pakistan karatu acan yakare duk karatunsa, haka Suka taso da Mahmud tamkar tagwaye sedai hali ba guda ba, Mahmud kadai ke iyawa da Ahmed se kuwa kanwarsa Hafsa

Mahmud yayi karatunshi a Mumbai acikin kasar india saboda haka lokacin2 suka ziyarci juna kasancewar babu nisa tsakanin Pakistan sa india kusan ma kasa yanki dayane, sunyi sa'ar  fito da kwali mai kyau tareda aykinsu ahannu.......

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 2鈨�0鈨�
Koda Ahmed yadawo daga kara2 har Hafsa tafara college, hjy na matukar tsoron Ahmed tun ranarda mahaifiyarsa nada rai tagayamata magana Ahmed yadauko cup din glass ya watsa mata shi aka kuma yadinga dukanta da kujera, dkyar uwarshi ta rabashi da ita,

Uwa uba karatun dayayi na soldiers shine karin bakin ransa kullum fuskarsa a tamke idan dai kinga dariyar shi to yana tareda kanwar shi Hafsa, wadda a duk lokacin daya kalli kwayar idonta yakan tuna mahaifiyarsa, Ahmed nada shegiyar zuciya amma me daya sha eviron drink zai dawo normal ,

Yatsani ka masa laifi kabasa hakuri, yafi bukatar kabarshi da bacin ransa domin basa hakuri tamkar kada da laifi ne agurinshi , abdallah kuwa babu abunda yakoyo a indiaa illah shasahanci da shaye2 se biyar mata, hakama amina tana Dan tabawa ma'ana tafaye soyy zamani wato romantic love

Hafsa kuwa baruwanta daga islamiyya se skull dinsu bata saurareni, kowani saurayi, Dukda ana ne manta, Sedai ta mutu son Mahmud amma batabari yagane ba, Sedai batasan tuni Ahmed yakamo tashar taba yadai samata ido ne kawai

Mahmud yanada kama da Ahmed farinsu daya sedai Mahmud yafi haske, Ahmed kuwa yasurka da ja, karatun da sukayi a india, sundauki al adunsu da dama example barin suma, Sedai yayi retouching dinta amma baya cirewa sekuma ta dace da fuskar sa, dogo ne mai faffadan kirji, yanada dogon hanci da karamun lips wadanda suke pink sosai kamar ansaka musu lipstick,

Sam Ahmed baya saka manyan kaya zai iya shekara bai saka manyan kayaba , ko ranar Friday sedai yasaka jallabiya fara, akwai shi da son kamshi ka tsantsainin tsiya, akwai shi da kyama mutane, bai dauki mace abakin komai ba, baruwansa da sha anin mata,

Shi aduniya baida wanda ya tsana irin Wanda yace yana sonsa, ko agurin aykin suka je kowani mission. Tokuwa ko commissioner na tsoron Ahmed saboda saurin zuciyarsa, akwai lokacin da gardama ta hadasu da wani captain abun yafara yabawa Ahmed haushi yaki sakar masa, binidiga kawai yafidda ya halbesa a kafa, indai agurin ayki ne suke to kowa kafa2 yake dashi, in kuwa agida ne belt ke ayki amina tasha dukanshi har ta gode allah

Yau tin safe baffa yatashi da ciyon kafa, Gashi yana son fita kiyo amma ba hali tin yana daurewa har yafara nishi, gwaggo tace baffan joda lfyrka kuwa yau senaganka kamar ba kajin dadi ne  , dakyar ya iya furta kafarshi, gwaggo duk ta gigice arude taje tasame hadi tagaya masa,  Yace mata shi bashida kudin kai shi asibity,  Gashi nan garin babu itace se daji balantana gwaggo  tahada masa magani

Haka tacigaba da zama dashi har yafara kasawa domin kuwa baya iya tashi komai Itake yimasa, ga kafar har tafara doyi domin kuwa ruwa take fitarwa abun bakyan gani, gwaggo tayi fita a titi tana neman taimako amma dkyar tasamu wanda yabata dari biyu itama kuwa gurin cin abinci gari da sugar yakare

Joda kuwa duk tabi tarame bata cin komai sedai tasaka mahsifinta agaba tayi ta kuka, haka zata rungume gwaggo suyita kuka, joda da bakar zuciya, ta fita daga gidan ganin yanda aka wulakanta ubanta da zummar zatayi aiki kona Menene tasamu kudi, shago2 take bi tana lekawa , tana neman taimako amma babu wanda yataimaka mata sedai akorata

Har tajuya daga wani katon shago naka Yan cosmetic , Sega wani babban mutun ya Parker da katuwar mota, tana daga gefe labe tana share kwalla, seda yagama siyayyar sa, sannan yace yarinya meke damunki kike kuka, kara fashewa tayi dawani kukan  , tace wai ku cikin gari bakuda imani ne bakuda tausayi zuciyarku bushash shiyace, Mutumin yace to wai me aka miki ne haka, toba baffana bane bashida lfy kafarshi naruwa tayi karuwa kamar hularka amma narasa mai taimakamun mukaihi gurin bokayen turai

Mutimin ya aza a dariya bokaye kuma, mai shagon yace alhj wannan fa, yar daji ce dubi kayanta ma da kwalliyar ta , joda tafusata shibai taimaka mataba amma yazo yana zaginta dukawa tayi akasa tadauko katon dutse tajefa masa aikuwa Sega glass din gurin  yafashe ,

mai shagon yace  babbar bura uba, wlh se an biyani kona kaiki station, mahaukaciyar banza, joda tace uwarka ce mahaukaciya馃槒 alhj kam yatsaya sororo yana kallanta, Yace yi hakuri manir zan biya kasan fulani da zuciya.........

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 2鈨�1鈨�
Alhj yabiya shi kudinsa kudin 30thnd  yace wa joda kibiyoni amota na zamuje gidana inshirya semuzo adauki baffan naki amota, akashi asibity koh!  Joda tayi shiru tana kallan motar tace ni zanjiraka anan yace a'a nibazan dawo nan ba, zan iya mantawa, takalli mai shago tace Dan allah bawon allah bakomai idan nabisa, munir yayi murmushi lallai wannan yarinyar akwai wautar fulani acikinta inba hakaba seda tagama masa rashin kunya sannan yanxu tazo tana tanbayar shi, Yace bakomai ay halinshi ne taimako

Cike da tsoro joda tabisa amotar, Shikuma se murmushin mugunta yake, seda Suka hau titin by pass sannan yadauko wata powder ya shaka mata, bata sake sanin inda kanta yakeba se bayan wasu awanni sannan ta farka ta ganta acikin wata motar tadaban bakowa aciki awani katon fili gurin mai kyau, ahankali ta buda inda taga ana budewa a shiga taji shi gam aikuwa tadinga bubbuga motar da karfin allah amma ina bamai jinta

Ahmed yashirya yadauki Hafsa sukaje dauko dad , Karfe hudu tabuga yakalli Hafsa yace dad ya iso, aikuwa Sega jirginsu ya sabka, aka gama duk wani shirye2 daza ayi, Ahmed yace 6ter sefa sunkai 30 mnt kafin Su fito, Hafsa tace abun haushi wlh bari indan sha ice cream, tafita ta siyo ice cream ta tsaya jikin wata mota tana sha gaf2 taji ana dukan motar jiyowar dazatayi taga joda kamar tayi hauka fuskarta duk taji ja

Ice cream din dake hannunta tayada ta sheka da gudu se gurin Ahmed tace bros c diz motor wata yarinya acike da alama satota akayi saboda daga ninta irin fulanin nan ne na daji fuskarta duk kwalliyar hauka ce, Ahmed yace a ina muje , Atare suka fito daga motar Tanuna masa, Ahmed yayi dannar ganbun har yagaji amma yaki budewa dole yayimata nuni da hannunsa datajanye yafasa glass din amma taki sunkai kusan minti goma amma taki janyewa Ahmed kuwa yafusata

Hafsa tace bros mezai hana kaballa kanbun yagalla mata harara , kafata karfece dazata bude wannan ganvun, Hafsa tace zaka iya bros ka gwada, mtsss yaja tsaki, hannunsa yasaka a aljihun wandonsa ya ciro bindina yasaita dai2 gurin key yaharba tuni ganbun ya bude yana fitar da hayaki , Hafsa ta karsa cikin motar taga yarinyar akwance tace bros tafa suma, Yace tomezan mata kuma ayanzu, Hafsa tace mutaimaka mata mana, Yace wannan kuma se inke zakiyi babu wani dalili dazaisa intava wannan najasar, Hafsa ta gyada kai, tace to kabani key din motar zan kaita hospital

Ahmed yace ar u mad, acikin mota na zaki saka mun wannan kazantar, Hafsa batasake cewa komai ba taciro wayarta takira driver tace masa maza2 yakawo mata motar a airport tana jira, Nan da nan kuwa Segashi yakawo mata, tasaka joda acikin motar tayima Ahmed sallama tawuce da ita hospital

Acan asibity kuwa joda seda tadau long time sannan ta farka tanata kankame jikinta, tana fadan daga zaka taimamun seka kawoni garin cire kai, Hafsa ta riketa tana fadan bashi bane kalleni, suna hada ido Hafsa taji wani shock itama kuwa joda dasauri kowannensu yajanye idonsa, joda tace Dan allah waye ke? Hafsa tace idan kinci abinci zan gayamiki joda tace ina wannan makashin yake?

Hafsa tace waye makashi kuma ? Joda tace wanda yake yawo da bunduga, Hafsa ta kyalkyale da dariya tace kintaba ganinsa ne, joda tace wlh kuwa Hafsa tace a ina, joda tace adajin mu anan tabata labarin fadawarta kogi ita kanta Hafsa ta tsorata amma tasan Ahmed zai iya wannan Hafsa tace yayana ne, kuwa soja ne shi isa yake yawo da bingida saboda tsaro da ceton jama'a yanzu ba gashi ya cece kiba, joda tace ehh kam

Hafsa tace meya kawoki cikin wannan motar kuma meyasa kike kuka satoki akayi ne, joda ta fashe da kuka mai ban tausayi, Hafsa tadafata tace kigayamun mana ahankali tagaya mata, Hafsa tace inbanda jahilci yadebeki yazakiga mutum yabiya miki dubu talatin lokacin guda batareda kinsan shiba kuma ki yarda dashi ai nakwarai sun karamta aduniya, kuma har in zai taimaka miki ai seya baki kudin alokacin tunda yana dasu amma seya jaki ke bakiyi wannan tunanin ba, joda tace kokadan cikin muryar kuka, hafasa tace yanzu inane unguwar ku inmaidaki, joda tace masallacin shehu ne, Hafsa tace ina ne masallacin shehu kuma?

Joda tace ai ance duk shine babba acikin garin nan, Hafsa tace wane gari kuma mukam nan bamuda masallacin shehu, joda tace asokoton nan akwai wanda baisan masallacin shehu ba, hafsa tazare ido sokoto kuma ke asokoton kike ne joda  tace ehh mana hafasa tace tabdi waynzu kina abuja ne, joda tace inane abujan, Hafsa tace tsakanin ta da sokoto tafiyar awa tara ne amma inaga ajirgi kukazo, tuni joda takurma ihu tazube kan gado. ........

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹FULANIN DAJI 馃巹
    馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
       馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 
          馃巹 馃巹 馃巹
             馃巹 馃巹
                馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 2鈨�2鈨�
Hafsa tadago joda tace karki damu yar uwa ba abunda zai faru dake se alkhairi yanzu kibari zuwa gobe , se a maida ki garinku, joda tace wayyo allah nah wlh gwaggo zata dakeni kuma inason ganin baffana, Hafsa tace to zaki iya biyar jirgi muje, joda tace Menene jirgi, oh tsuntsu mai tashi zama,  Hafsa tadanne dariya tace ehh shi, joda tabata rai kwarankwatsa bazan shiga wannan mugun abun ba na yahudawa, Hafsa dai da taga abun bana karewa bane taje tasamu doctor daya duba joda tace masa Dan allah Yayi mata allurar bacci

Haka kuwa akayi bayan Anyi mata allurar, Hafsa takira Ahmed takoro masa bayani haushin yarinyar yaci kashi yace yanzu akan wannan kucakar zakiyi missing din dad kije kaita gida why not da bazaki barta ba ay wannan ma dakikayi taimako ne,

Hafsa tace hava Bro yanzun fa idan babarta wlh zata iya Fadawa wani mugun hannun daban "plss give me one chance "  Ahmed yace shikenan kiyi hankali dakanki kuma zanturo abbas yayimuku komai kina kaita gun iyayenta kijiyo kada kisa ba mun kinfi kowa sanin halina, Hafsa tace tnkuu bros insha allah bazanyi abunda badai dai ba,

Haka kuwa akayi abbas yayi musu komai cikin minti ashirin suka bar abuja se skt har suka isa joda bacci take mota Ahmed yatura a airport din skt, tadaukesu se unguwar masallacin shehu, jin atsaya kiyyy da mota ne yasa joda farkawa , tagwale ido tana kallan unguwar juyowar dazatayi ne taga Hafsa na mata murmushi, tace to yanzu gamu a unguwar ku seki nuna mana gidan, joda tace yanxu kwananmu nawa muna tafiya, Hafsa tace kodaya ko awaya biyu bamuyi ba yanzu dai kinuna mana gidan ahankali tanuna gunda almajirai ke daukar karatu, Hafsa tace tnk god muje koh

Ganin taron jama'a yasaka joda kaduwa , tace lfy kuwa dasauri tashiga cikin gidan carab idonta yafada kan gwaggo tana rungume da hannayenta hawaye nabin fuskar ta Fadawa tayi kanta tana gwaggo bari kuka mana jikin baffan ne koh insha allah zaiji sauki,  gwaggo takara fashewa dakuka tareda kankame joda ajikinta, tace joda ina kika je tin safe baffanki yayita Kiran sunanki kafin yacika, joda batareda ta fahimci yacika ba, tace gwaggo yana ina in gaidasa, gwaggo tace joda zoki zauna wanda yafimu sonsa yakarbi abunshi, joda tace wai mekike son fadane haka, gwaggo tace wannan waye kuma Tanuna Hafsa

Hafsa takaraso tazauna, joda tace gwaggo itace wadda ta taimakamun dana fada hannun wani azzalumi nan tabawa gwaggo labarin komai, gwaggo tace hava joda muda muke baki agari yaushe zakije neman taimako bayan Bakisan kowa ba, hafsa tace ayi hakuri dai allah yaji kan shi da rahma, joda tafashe da kuka gwaggo baffana yarasu ne, gwaggo tace ya muka iya joda baffanki yatafi gidan gsky sedai muyi masa fatan dacewa

Hafsa ta tausaya musu sosai, gwaggo tace joda ki shirya mana kayanmu zamu bar garin nan, yau baffanki yace mufita daga gidannan kada Su hadi Su salwantar da rayuwar mu, Hafsa tace yanzu to idan kuka bar nan garin ina zakuje, gwaggo tace neman aiki ba ance kunan cikin gari kuna daukar mata aiki ba, hafsa tace haka ne amma kuyi hankali mutanen duniyar nan se a slow tadauko kudi sunkai 20k tabasu tace gasu kurage zafi nizan koma gwaggo akan murna kuka takara fashewa dashi, joda taraka Hafsa har mota tanata daga mata hannu sannan takoma ciki

Hafsa kuwa bata koma gida ba se kusan isha'i cike da gajiya ta isa gida, tana ta zumudin ganin dad dinta, Ahmed taci karo dashi a kofa yana fitowa yace mata sannu da wahala, dariya tayi hava bros yade wahala, nidai ina dad, Ahmed yace kinyi  late yashiga bacci sedai gobe,  ta tabe baki kai bros, Ahmed yayi wucewarshi yabarta atsaye

Tin 6 Ahmed yaje yatada Hafsata ta tashi tashiga kitchen tareda mai girkinsu akafara hada abinci kala2 zuwa 8 komai ready har gidan angyara takoma dakinta tayi wanka ta shirya , sannan tashiga dakin Ahmed tace bros zan gyara dakin, bai amsaba kuma batasa ran zai amsaba, toilet yashige itakuma tashiga gyaran dakin har tagama baifo ba seta dauko wani jarida tana dubawa kusan 15 mnt se gashi yafito daure da towel babba ya yaba wani sama Hafsa tashige toilet din ta wanke tass ta kunna turare ko ina sannan tafita

Ahmed yakira dad awaya yace dad kaimu ke jira a dining fah, dad yace ina zuwa, kowa ya hallara a parlour dad kadai ake jira, yafito cikin shigar alfarma, yajanyo kujera yazauna, Hafsa tace mrng dad ya hanya, lfy lau hafsatu , ina kika je jiya? tace dad idan mungama break zan gayama yanzu lokacin karyawa ne, dad yace wato kema kindauki akidar yayanki komai yanada lkcn shi kenan "

Murmushi tayi to dad ya kake son inyi ba kyau zance alokacin da ake cin abinci, Ahmed yace to yanzun ma mekike yi ne ? Hafsa ta dukadda kanta tacigaba da cin abunci,

Gwaggo sungama hada kayansu kaf sukayi wa hadi sallama , se tasha inda ake shiga mota, tsaye sukayi Dan basu San motar dazasu shiga ba, sudai sunji anata dadan kano2 katsina, kaduna, gwaggo taduba taga motar da ake cewa kaduna tafi mata dayawa Dan haka itama tashiga ciki , tarungume joda seda motar tacika kaf sannan suka daga

Ankai inda ake tsayawa saboda adan Ci abinci amma ina gwaggo tace bata cin komai joda kuwa najin yunwa amma tadaure tasha, ruwa kadai, matar dake gefensu na lure da yanayinsu aranta tace Tabbas akwai damuwa atattare dasu kamar ma basu yarda da kowa ba,

馃巹FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 2鈨�3鈨�
Matar tayago masa da malt tamikawa gwaggo tace yar uwa ungo bismillah,  gwaggo cike da fargaba tace a'a mungode, matar tace hava keko ba a maida hannun alkhairi baya, dole gwaggo ta karba tabawa joda cikin sauri kuwa joda tacinye Su tass,

Matar tace boyar allah meyasa baki siyama yarki abinci ba bayan kinsan tanajin yunwa, gwaggo tace toya zamuyi tunda yn kudin mu ba yawa ne dasu ba, matar tace to yanzu ina zaku, gwaggo tace munfito neman na kanmu ne

Matar tace idan na fahimta aiki kike nema ko muhallin zama, gwaggo tace ehh, matar tace bakida matsala da wannan ni dinnan yara da manya nake daukowa a kauye na kaisu gurin aiki garuruwa za abaki muhalli mai kyau iyakacinki kiyi goge2 ko kuma wanke2 da sauransu inkuma kin iya girkin zamani shikenan, amma da alama se an gyara ku akwai dinbin kauyanci acikinku,

Gwaggo tace indai zamu Ci musha da muhalli to wlh komi nene zamuyi bama bukatar ko sisi indai muna da wadannan ababen, matar tace inafa dole in wata yayi abiyaku naku salary din, gwaggo tace ina ruwan riba goma

Haka dai suka cigaba da fira har Suka isa kaduna, matar takirga kudin gwaggo tacika mata tabiya ta tajata tace zo muje gidana ,haka kuwa akayi suka tare taxi se gidan matar gidane babba mai kyau, Filin gidan kadai yana wani gida ga mota kusan ukku acikin gidan , har parlour Suka je, matar tace kuzauna ina zuwa , wanka tayi tacanza sutura sannan tafito takawo musu ruwa da abinci dakyar suke cin abuncin saboda basu sababa , seda ta tabbatar sun koshi sannan tace subiyota ta nuna musu masaukinsu,

Katon daki takaisu ciki mai katuwar katifa tashiga nuna musu abubuwan yadda suke toilet tashiga dasu tana nuna musu yadda ake amfani da komai Gwaggo kam imani yakamata joda kuwa ta matso safiya  tawaye taje toilet din wani dadi yakamata jin ta bisa kaifa mai shegen laushi, ga bargo suyi rufa, salloli sukayi sannan suka kira safiya

Karfe bakwai matar tashigo tasamesu har sun tashi sukayi mata ina kwana gwaggo nata dada godiya, matar tace bakomai ay yiwa kaine ni sunana hjy binta inada miji yana abuja gurin wani aiki dana guda salim yana America gurin karatu, gwaggo tace allah yabarku da mai gidanki yakara zaman lfy ameen, hjy binta tace joda kinyi brush kuwa, joda tayi shiru Menene brush kuma hjy binta tace zo kiga tajata se toilet tazuba mata colgate a brush sannan tabata tace kinga yadda zakiyi tanata nuna mata kafin tafito kam  rigarta sharkaf da ruwa

Joda tace gwaggo kinsan abunnan danayiwa hakorana allah dadi ne dashi kamar minti yake, nikuma se tsotsewa nake, gwaggo tace to uwar kwadayi, hjy binta takawo musu tufafi joda kuwa nata duk kananan kaya ne, se dadi takeji ita ke nuna mata yadda ake sakawa da yadda ake cirewa

Ahankali take nuna musu abubuwan zamani, yanzu dai sundan rage tsoro da kyauyanci, tinda har TV suke kallo lfy lau, hjy binta kuwa batayi kasa a gwiya ba tacigaba da wayar musu dakai seda ta tabbatar yanzu basuda matsala da komai sannan tashiga nuna musu yadda gyaran gida da yadda ake tsara parlour sundau kusan wata tana nuna musu abubuwa asara kam tashata agun joda saboda joda akwai barna kamar mage haka take

Yanzu suna kan girki ne tinkan Su semo har zuwa abuncin zamani yanzu komai sun iya itada joda wata biyu kenan, hjy binta tace to gwaggo yanzu ko yaushe zaku iya barin gidannan saboda yanzu nasan kun kware akowani fanni sannan kuma ni kunga tafiya zanyi so kafin in wuce zan nemo muku gidan aiki mai mutunci joda tace hjy mu munfi son zama dake kinfi kowa kirki aduniya hjy binta ta kyalkyale da dariya tace injiwa keko joda har wanda suka fini akwai

Ahmed zaune a garden yana shan iska yana kallon tsuntsayen dake wasa agurin zuciyarshi fall, gefensa tire ne shike da kayan marnari, kamar ance duba ya waiga bayan sa mezai gani, amina ce sanye da base iya cibiyarta se wando baiwuce gwiwarta ba, rike da kujerar roba zata shiga ruwa, baki yasaki yana kallanta Keee yadaka mata tsawa, seda ta tsorata Dan batama San yana gidan ba

Wani irin iskanci ne zaki zauna ma mutane tsirara haka, Nan gidan kine ko dakin ki, amina tace to naga dai ai bamai shigo mana gida, Ahmed yamike tsaye zanci ubanki wlh, muba maxa bane ko angaya miki yahallata ko uwarki taganki ahaka ballantana mu maza

Amina ta murguda baki Kaji dashi can tafada cikin ruwa se ihu take, Ahmed yafusata ainun, ya zare belt dinsa ya nufi swimming pool din hannu sa yazura yacabko gashinta tuni tabuga ihu kafarsa yasa yabuge mata baki seda yamata liss sannan yabarta agurin

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 2鈨�4鈨�
Hjy binta tashiga tunanin inda zata kai  Su gwaggo batareda sun takura ba gidan dai da bataso dole can zata kaisu, tagayamusu Su shirya zasuje gidan aikinsu ba musu suka shirya tin safe bayan sunkarya suka dau hanyar abj , hjy binta tayi horn mai gadi yabude gate din saboda yasanta bata bukatar wani bincike akai,

A parlour Suka yada zango, hjy binta tadauko wayarta takira hjyr gidan, amma kafun tafito sunfi karfin minti talatin, sanye yake cikin riga red se wando 3 Q yasan ya Farin glass hannunsa rike da system yafito daga dakinsa,

Hjy binta tace a'a Ahmed na baida go fuskar shiba seda yakai bakin kofa sannan yace ehh, tace ygd yakaratu, cike da haushin tambayoyin yace lfy, batareda yajira wani que ba yafice , gwaggo tace wannan kuma fa, ?Hjy binta tace dansu ne shine babba, gwaggo tace to allah yakauta, ameen

Hjy tafito se wani dagawa take tasamu guri tazauna, tace hjy binta yagari , hjy binta tace lfy lau, hjy dama bawani abu bane yazo dani wadannan dakike gani baki ne daga daji suka fito kuma mijinta yarasu bada dewaba amota na hadu dasu zuwa zauna gurina kusan wata biyu da Yan Kwanaki zuwa yanzu sun waye suna iya kowane ayki na gida, shine nakawo miki Su ko akwai bukatar Yan aiki nan gidan,

Hjy tace no binta bana bukatar Yan aiki wadanda ma ke gidan wlh sun isheni, binta tace to hjy kozasu zauna gunki ne kafin in dawo daga zaria, hjy tace binta bana mgn biyu fa, hafsa dake saukowa downstairs duk taji abunda suke tattaunawa, taje  tasame Ahmed tamasa bayani yace tomezan musu ne kiji ance fulanin daji ne me zamuyi dasu ne, Hafsa tace yaya taimako nefa kuma binta tace data dawo inba ma bukatar Su zata koma da abunta

Ahmed yace Hafsa stay away 4rm here, hafsa da takaici yacikata garden dinsu kawai tawuce cike da takaicin halin yayanta, Ahmed kuwa glass dinsa yasaka ya nufi parlour din hjy nazaune tabawa TV amana, Yace lfy wadannan kuwa? Hjy tace aiki suke nema kuma bama bukata munada isassun ma'aikata, Ahmed yace wannan ba kawar ummah bace, binta tace ehh nice Ahmed ashe zaka shaida ni, Ahmed yace kije kawai za'a basu ai kinyi, binta tace nagode sosai Ahmed allah yaji kan mahaifiyarka ameen

Hjy tace yazance bana bukatar Yan aiki sannan kuma kadaukesu, Ahmed cike dagadara yace kozaki hana ne nan gidan ubana ne inada right din duk abunda nakeso , hjy tace kai kake da wannan right amma sauran basuda shi, Ahmed yace zaku iya jira inkira kanwata tamuku masauki kunjiko , se a lokacin joda tadago fuskar ta takalle shi, 馃槼 Iye makashi tuni ta kwala ihu, Ahmed yadafe kunnuwansa dajin wannan ihun abunda ya tsana hanyar dakinsa yayi se faman tsaki yake

Binta tace lfy ke joda gwaggo tashiga jijjigata ke lfy, tace gwaggo wlh mubar nan gidan, gidan  makashi ne shine Wanda yakashe kada aruwa shine Wanda ya harbi ganbun mota kadan in mutu, binta tace kai joda akwai shiririta wlh yoshe akayi haka wanda baya ko fita kullum yana dakin shi in kuwa ki ganshi yafita Tokuwa gurin aiki zashi, dole joda tayi shiru cike da tsoron zama agidan,

Hjy tabar parlour tayi dakinta, ba'ajimaba Sega  Hafsa tafito, Lah inna kece dama gwaggo tace nan ne garinku dama, hafsa tace sosai nanma gidanmu ne ina joda, Gwaggo tace ta fita tayo fitsari, Sega ta kuwa ihu tasaki taje gurin Hafsa tace yar uwa, hafsa tace ashe allah zaiyi mugamu , hjy binta tayi musu sallama tawuce cike da jin dadi Dan tasan Hafsa akwai kirki

Seda Suka sha fira sannan Hafsa ta fita dasu zuwa sashin masu aiki tanuna musu masaukinsu, sannan takoma dakinta ,dasafe tazo tanbayar Su abunda suka iya koda ta gwada Su sunsan abubuwa da dama, tayi matukar mamakin ganin yadda suka Dan rage hauka da kauyanci

Joda ita ke taya mai gyaran gidan aiki gwaggo kuwa kitchen takebin mai aiki suyi tare, kwarai da gaske suke jin dadin zama da gwaggo saboda batada kissa ko kadan komai tsakani da allah take yinsa,

Tin ranar joda batasake ganin Ahmed ba sedai tayi ta jin kamshin sa idan yabi ahanya , kullum da jacket dinshi take kwana ko ana zafi seta sakata take iya bacci itama kuma Batasan dalilin hakan ba, tofah jama'a kuji joda meke damunta ne oho 馃槦

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
   馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
      馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
        馃巹 馃巹 馃巹
           馃巹 馃巹
              馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 2鈨�5鈨�
Joda har ansaba da gida ko ina shiga take har cikin parlour abunda sauran masu aiki basayi, hafsa tasa ta ajiki sosai, haka zata yi tadibar kayanta tana bawa joda , Yauma kamar kullum tafito daga kitchen tanata wake2 abunta hanunta rike abunci, karab taji taci karo da mutum, gabanta yashiga dukan 3 Dan koba ta dagoba tasan ko waye , tsawa yadaka mata keeee mahaukaciyar inace kina gani kin takani kuma kin wani tsayawa sororo , jikinta yashiga bari tace Dan allah kayi hakuri wlh banganiba, mari taji mai kyau, to ubanwa zai goge mun talkamina,

Dasauri tacire Dan kwalinta tashiga goge masa kafarsa bata ankaraba tashar awa wandonsa manja,  yana dubawa yace bura uba wlh sena karya yarinyar nan, jikinta yakara bari tafara kuka, tashi tayi zata gudu taji ancabko gashin ta, kalansa take ido cikin ido, Yace ni zaki yiwa iskanci shin waima ubanwa yakawoki nan gidan shegiya mai fuskar jaba, joda tace Dan allah kayi hakuri ba a kaine ka karbemu aiki ba, yakara fusata, Dan ubanki yaushe kika taba ganina, yawulgata dakarfi, se asamam kafar wani

Durkushewa tayi tana kuka cikin muryar Su ta fulani tace Dan allah kiyi hakuri wlh bada gayya namiki hakan ba, wanda tafada kan kafarshi yadagota idonta arufe yake tana hawaye jikinta se karkarwa yake, joda kuwa seta rike masa hannu, tana Dan allah kayi hakuri,  abunda ya tsana kenan kalmar hakuri, Tasake cewa dan allah fah nace, wanda tarike yadaka mata tsawa you shout up,  dagowa tayi tana kallan sa tuni ta ware ido ganinsa cikin kayan soldiers, ubanwa yabaki izinin shigowa parlour nan, Iye, mari yakai mata ba dake nake mgn ba, kucakar banza, hannunta yacire kan nasa, seyaga ta Su lale ashe har tasuma, tsaki yaja ya tsallake ta yawuce,

Abdallah yace kai tafa suma, Ahmed cike da tsanar zancen yace to mezan mata, abdallah yace tsawar dakamata ne kana abu se kace wani  lion, Ahmed yace shine ai, yayi gaba abunsa, abdallah yadauko ruwa a fridge yazuba mata, ahankali tabude idonta , tana ganin sa tamaza tarufe, abdallah yace kuji shegiyar yarinya to ai sekiyi ta, rufewa ya hankadata yawuce sama ,

Ahmed kuwa tubewa yayi yasaka jallabiya zai shiga wanka kome yatuna sekuma yafito dasauri, a parlour yasameta ta kudundume guri guda se rawar dari take, Yace kee wai nan parlon ubanki ne da bazaki fita ba, joda takara matse jikinta, tadanne kunnuwata, abun se yakara fusata tashi , wato bata son jin zancensa kenan, Yace kee wlh zan karyaki kibar nan parlon nace, rerafe tadinga yi har takai bakin kofa sannan tawazga aguje se dakinsu tafada kan gado tana cigaba da rawar dari,

Hafsa tadawo daga islamiyya tabiya dakinsu joda, a parlour tasamu gwaggo tana yiwa husaina kitso, tace inna ina JODA taje, inna tace kishi ga daga ciki, Asaman gado tasameta ta yaye bargon ke lfynki kuwa, joda tace zazzabi kedamuna, hafsa tace Ayya sannu kinsha magani kuwa , joda tace a'a Hafsa tace to bara nakawo miki mgn kinji koh,

dakin Ahmed tashiga tayi sallama yabata izinin shigowa dakin, kan gado tasamesa kwance yana shan wakar Kenny G , tace bros maganin zazzabi zaka bani, kina zazzabi ne? tace no bros joda ce ba lfy, Yace you get out banasan renen hankali, tace bros yarinyar daka..... Ahmed you yadaka mata tsawa shout up  , bana bukatar sanin kowacce magani bazan bayar ba dz oll

Hafsa tafita daga dakin cike da haushi batama koma dakinsu joda ba, sallah tayi tayi wanka tasake kaya sannan tasauko kasa danyin lunch, amina na kan 3 star tana kallon star movies , tawuce ta ta hau dining tazuba crab cakes da honeydew peach cooler, tana ci cike dajin dadin abincin, tace amina wlh duk zaman husaina mai girki bata taba mana irin wannan ba, amina tace to waya tanbayeki da iskanci

Hafsa tace kece da iskanci wlh daga magana zakice mun da iskanci, amina ta taso ni kike gayawa mgn, hafsa tace angaya miki tsoronki nake, tuni hafsa takai mata mari abaki bata sauke hannunta ba, hafsa takai mata nanko fada yakaure atsakaninsu,

Ahmed dake son yin bacci yahaniyarsu ta tada shi, fusace yafito rike da belt, turus yayi ganin Su hafsa na danbe , yadunfaresu tuni hafsa ta sake amina tayi hanyar waje tsalle daya yayi yacabkota yashiga zuba mata belt Dan ubanku da girmanku zakuyimana danbe agida Iye seda yamata liss sannan yabi amina da tun tuni tayi sama tasakama dakin hjy key

Hjy tace ke lfy kika fado mun daki ko sallama babu,  amina da idonta keta wani wuki2 tace bros Ahmed ne zai dakeni, hjy tace to me kika masa ne? Amina tace wai yar iskar kanwar shi ce take gayamun mgn nikuma na bibbigeta shine zai dakeni itama yazaneta, hjy tace to ai kinmun dai2 kada kitaba yarda taranaki.........

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 2鈨�6鈨�
Ganbun dakin aka bugo dakarfi bugu daya yayi masa da kafarshi amma yabude se huci yake , hjy tace wlh karka kuskura kayaba mun yarinya, cike da tsana yake kallonta koke idan kika kara mun zan dakeki balantana yarki, ke kuma ki kawo kanki inda keki inba hakaba wlh idan nakamoki da hannuna senayi miki wanda yafi wanda nayi niyyar miki, komawa tayi bayan hjy tana hararanshi,

Ahmed yadunfaresu, hjy takara tareda mike hannayenta, Ahmed yace kijace wlh ko in hada dake, hjy da ranta yagama baci tace shege kake idan baka dakeni ba, tuni Ahmed yacabko ta tareda wulgata se kan gado yajanyo amina yashiga dukanta tin tana kuka har takasayi sannan ya yada belt yawuce yabarsu,

hjy tayi ta kururuwa har tagaji, daga karshe tadauko phone takira abdallah ta tsara masa karya da gaskiya, abdallah kuwa yana zana wata exam baisan tym dinda ya yaga papers dinba yabar hall din dasauri baima tsaya Jan mota ba yahau Dan achaba yana zuwa gidan yabude ganbun parlour dakarfi, can gefe ya hango hafsa na kuka bakinta se jini yake, yabuga tsaki yawuce wato ko kanwarshi bai bariba, tun kan ya isa yakejin kukan amina

Rungume da hjy yasameta tana kuka, abdallah yace hjy tell me meya miki hadda ke yadaka, amina tashare kwalla wlh bros hadda ita yayita zuba mata belt, abdallah yace to wlh yau gidannan za'ayi kashin kai , hjy tace look son kada kayi fada dashi wlh kasan yadda zuciyarshi take tamkar ta kafiri wlh zai iya illata mun kai abdallah yace komai zai faru sedai yafaru amma wlh ba shegen daya isa yataba uwata yakwana lfy

Fita yayi daga dakin yadum fare dakin Ahmed amma me seyaji kofar a kulle haushi duk yaci kashi juyowar da zaiyi yaci karo da dad dinsu, dad yarike kuqu yace kayo shan ne shi isa naga kazo zaka ballamasa kofa , abdallah yace dad bansha komai ba amma wlh za'ayi kashin kai agidan nan, dad yace subhanallah Abdullahi mekake fada haka, abdallah yace yes dad , Ahmed yace shege kafasa nida kai , dukansu suka juya suna kallonsa yafito daga kitchen rike da cup din coffee,

Abdallah yadunfaresa, Ahmed ya ajiye cup din coffee, yatartara hannun rigarsa , dad yace muhammad kada kasoma kaima Abdullahi kada ka fara wlh dukanku zan sabamuku kusameni after magrib, dukansu kowa yakama gabansa, hafsa kuwa tana tashi taje tahada ruwan zafi taga sa jikinta, se baccin wahala, amina kuwa ruwa hjy tahada da towel tagasa mata jikinta tahada mata tea tasha sannan tasauya mata kaya

Bayan magrib dad yabukaci ganin Ahmed da abdallah , yadau few minutes sannan yace, Abdullahi lfy kake neman fada da yayanka abunda baka saba yiba ? Abdallah yace katanbiyesa mana , dad yadaka masa tsawa, naki na tambiyesa kai dashi wanagani , abdallah yace dad ya za'a yi ace wai Ahmed yana dukan uwata ina raye in kyale ai wlh bazai yuba , dad yace ya isa kai muhammad meyafaru

Ahmed yazayyane ma dad komai yakara dacewa, dad idan yayi yunkurin tabani da sunan wai zaiyi danbe dani, am so sorry ku kunsan abunda zan iya yi dawanda bazan iyaba yana kai nan yafita dad yace muhammad na sallameka ne, Ahmed yace sorry dad ina bukatar hutu ne idan inajin wadannan abubuwan komai zai iya faruwa so allah ya huci zuciyarka , abdallah yace ahaka dad za kace mun yafini kirki dubi yadda yake gaya maka mgn sekace.......dad yace ina ruwanka tashi kabani guri kuma wlh kaji na rantse idan katada fitinar nan wlh sena batamaka rai

Ahmed dakinsa yafada kan gado yana maida nunfashi, gani nayi yatashi da karfi yadauko eviron drink yasha nan dannan yaji normal wayarshi yadauko yakira Mahmud, Mahmud yadaga man yatake ne, Ahmed yace mod kazo kadaukeni ina bukatar hutu ne bana bukatar zama agidan, Mahmud yace ok ina zuwa ko bai tanbaya ba yasan an taba Ahmed ne

Mahmud yafito daga motarshi, yakira Ahmed yace gashi aharabar gidan, ko minti biyu ba ayiba Sega Ahmed yashiga mota,  Mahmud yatada suka bar gidan se wani guri mai kyau nidai nakasa gane gurin kona Menene nadai ga decoration yayi yawa agurin mutane dai dai ne agurin kowa yana harkar gabanshi

hafasa tasame joda tace joda zoki gaida dad dina, joda tace a'a Hafsa ni ina tsoron in hadu da wannan yayan nakine wlh bashida maraba da nasara, hafsa tace ke baya nan, dakyar hafsa tashawo kan joda suka je, har dakinsa suka samesa yana karatun jarida, hafsa tace dad wannan itace naje gurinsu sokoto, dad abun tausayi babanta yarasu,  dad yace allah sarki allah yajikanshi ameen, joda tamike tace muje hafsa, hafsa tace kedai bakiyiba wlh daga zuwa, dad yadauko kudi yabata tace sam bata San zancen ba yayi yayi taki karba tace tagode

Mahmud yakalli Ahmed yace man wai yaushe zamuyi aure ne nifa nagaji dazama ahaka,  Ahmed yace mekarasa da zakayi aure, Mahmud yace tab ni gsky aure nakeso abunda matarka zata maka ba kowace mace zata maka shiba, Ahmed yace tomeka rasa ne arayuwa, Mahmud yace ahhh.....ina bukatar kadaituwa ne damace, Ahmed yace wannan kuma kai yashafa, Mahmud yace kaifa bai shafekabane?  Ahmed yace kaga bana San wannan iskanci abar zancen kawai, Mahmud yace niko zanga randa Ahmed zaice wa mace ilove you , Ahmed yace bakuma zaka ganiba

Mahmud yace to bakasan babies ne kenan? Ahmed yace idan ka haifa naka ma x ok, Mahmud yace kayanka kenan bazaka ji abun ba, Ahmed yace kai bansan bura uba wlh, Mahmud yace allah yashirya ka da girmanka kake zagi, Ahmed yace kada kasa ke mun wannan zancen ka naji koh..........

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
 N@ B aleeyu 馃挄 page 2鈨�7鈨�
Joda tace hafsa kikaini dakinki ingani hafsa tace to muje yanzu ma , joda tace yayanki bashi nan, hafsa tace eh muje kawai hafsa tarike hannun joda suka shiga parlour sukayi sama, a dakin hafsa joda se ihu take ganin yadda dakin hafsa yake tamkar a TV, seda Suka gama tsiyarsu sannan suka sauko kasa gurin saukowarta ne tahadu da amina, amina tadinga yimata kallan wulakanci, ke ubanwa yabaki izinin shigomana parlour kaxama kawai kucaka, tuni idon joda suka cika da kwalla, hafsa tace ni naba ta izinin shigowa

Amina taci kwalar joda ta hankadata kasa goshinta yafashe tuni joda tabare baki, dai2 nan Ahmed yadawo, dafe kansa Yayi oh god wai wannan wace irin yarinya ce kullum zai hadu da ita kuka yake ganin ta nayi, yadaka mata tsawa kee uban me kike a parlour nan, tuni jikinta yadau bari yakankame kujera hafsa tasauko kasa tace joda zo muje ciki, Ahmed yace gidan uwarki zataje koya, shegiya,  Yace kee wlh idan nasake ganin ki a parlour nan sena kare ki,  amina tace yayi dai2 bros shi isa nake son......bata karasaba yace zan ballaki ina magana kina mgn

Yasaki kallon joda da ke makyarkyata yace kee bazaki bar nan gurin ba senaci ubanki joda kam har fitsari tasako, Ahmed ganin tamasa banza yasa yayi wulgi da rigarshi ya dunfaro ta, joda dakejin kamshinsa nakara matso wa takara runtse idonta, cabko ta yayi da niyyar kadi da ita waje, seyaga tana laudi kamar matatta tsaki yaja yasaketa da karfi, Wata irin ajiyar zuciya tayi sekuma tayi lamo kan carpet, hafsa tabuga kalima bros jifa yanda kasako yar mutane akasa, Ahmed yace kema wlh nakusa kakkaryeki idan nasake ganin kin shigo mana da wannan kucakar acikin parlour

Amina dake tsaye tayi murmushin jin dadi, tawuce abunta, hafsa tarasa yanda zatayi da joda dakyar ta da gata ta kaita dakinsu tayi sa'a gwaggo na sallah, ta tsaya har tagama sannan tace ma gwaggo faduwa tayi gwaggo tace oh ni gurin rashin ji koh, gwaggo tana dubata tace amma dai taga wani abun tsoro koh, rabenta da irin wannan yanayin tun randa tafada kogi a dajin mu se shekaranjiya tace mun wai taga kwado ne,

Hafsa tayi shiru to kadai Ahmed dinne tagani shine ta boye mata tace kwado, Su ina sukaga kwado, wanga gidan, hafsa tace gwaggo yanzu ba abunda za'a mata takoma normal , gwaggo tace tomezan mata tunda nan ku bakuda itace ballantana in hada mata magani , hafsa tayi tagumi tana kallan joda tace to gwaggo Dan rufeta kamar zazzabi ne ya rufe ta haka kuwa akayi gwaggo tarufeta tayago kyalle ta dora gurin da goshinta ke fitar da jini

Tin ranar joda batasake gigin zuwa parlon Su ba sedai hafsa ta cimmata Su sha fira abunsu, gwaggo tace joda nikam ba makaranta a unguwar nan dazaki rika zuwa ni banga amfanin zamanki anan ba , joda tace to gwaggo sedai in hafsa tazo musa tanbaya, haka kuwa akayi joda ta tanbayi hafsa, hafsa tace suje islamiyya dinsu yafi sauki, hafsa taje tasame Ahmed tace bros I need help plss, Ahmed yacire glass dinshi yace to ina jinki, cike da tsoro tace bros joda ce......hannu yadaga mata bana bukatar duk wani abu daya shafeta kibar mun dakina kawai, ba musu tafita cike da haushin abun to ita yanzu ina zataje ne?

Abdallah yafado mata a rai , dakinsa ta nufa tana adduar allah yasa bai sha komai ba, takuwa yi sa'a yana nan lfyqlw ahankali tagaidashi ya amsa tareda tsare ta da ido yana son jin abunda ketafe da ita, guri tama kanta tazauna, bros Dan allah joda ce keson asaka ta islamiyya kuma kaga islamiyyanmu dole se ubanka ko wani nmj yasaka hannu ake karbarta shine naxo Dan allah kataimaka wlh maraya ce kamata komai nasan zaka iya

Abdallah yagalla mata harara Ohh yayanki ya koroki shine ni zaki zomun, shinma waye joda?  Tace plss bros nasan kafi Ahmed tausayi, wannan yarinyar da aka daukesu aiki last time, abdallah yace kan uba yarinyar da hjy tace bataso yayanki yanuna mata isa, to wlh ko karye ta zanyi kibacemun dagani ba abunda zanmata wlh sumuy2 ta tashi tabar dakin

Haka tasame joda tace mata se karshen wata za'a fara karbar new students, bayan kwana biyu shugaban makarantar Su yakira hafsa yace yana ana bukatar dalibar tazo dan amata enterview hafsa bayadda batayiba taji waya saka hannu amma malamin yace bai shafeta ba bata kawo kowaba illah abdallah Dan tasan shi da tausayi sabanin Ahmed...........

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
   馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
      馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
          馃巹 馃巹 馃巹
             馃巹 馃巹
                馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 2鈨�8鈨�
Hafsa tasamu joda tamata bayanin komai tace tashirya ran asabar zasu fara zuwa domin a gwada karatun ta , tanason zuwa tayi wa abdallah godiya sekuma tafasa, tace nasan ma zaiyi domin shi baidauko halin hjyr Su duka ba hasalima Itake kara turasa ga aikin da bai daceba

Joda tafito da katuwar kula zata kaima masu gadi da drivers abincinsu tafe take tana wakokin Su na fulani, tana shan alawa, doguwar riga ce ajikinta wadda hafsa tabata kanta sanye da hula kanta kuwa kitso daya aka mata yaxubo har kan gadon bayan ta,

 sallama tayi musu mai gadi yakarba tareda fadan a'a yar fillo yau ke aka bawa kular ashe dai kinyi karfi, murmushi tayi tace kaifa kaci ka tsokana ita wannan kular ce bazan iya dagawa ba ta ajiye tajuya har tayi nisa yace kee yar fillo ba tire kodaya joda ta dafe kai oh ni zainaba wlh namanta bara nakawo muku

Tajuya aguje tana dariya, se jinta tayi kamar tafada kan wani abu dago kanta tayi abunda tagani shine yai bala'in firgita ta, tuni ta San kare guri guda takasa motsi, kallo daya tayima idonsa tuni fitsari yazo mata, rike kugunsa yayi yana mata kallan wulakanci kamar wanda yaga kashi ,

itakuma tariga ta sankare ko motsi batayi, hararar dataga yana mata ne yasata rufe idonta, tareda rufe kunnuwata, Ahmed abun yabasa mamaki wai Menene wannan jakar take nufi batasan jin muryarsa ne batasan ganinsa shine dalilin dayasa take rufe idonta da kunnunwata idan tagansa

Karasowa yayi kusanta azatonsa zata gudu seyaga taki motsi, kafarsa yasa yataka ta, da shegun takalminsa  huuww taja iska hawaye suka cigaba dabin fuskar ta idonta arufe, Yace Keee ni sa'ar ubanki ne dazaki rika bi hanyata nan ba'a gayamiki gurin zaman mota ta bane ba uban dake binsa,

ko tsuntsu bai isa yabi wannan hayaba nabarsa balantana mutun, dakyar ta iya hada kalmar Dan allah kayi hakuri , Tau 馃槼 batasan abunda yatsana ba kenan,  Ahmed kee how dare you " ni ni zaki....sekuma yayi shiru ganin tanata langwadi da alama kasa tayi idonta se lumshe wa yake

Timm kakeji tafadi kasa, somammiya , tsaki yaja wannan yarinyar wlh na tsaneta bana San ganinta shegen kukan tsiya, tome ma yamata ne dazata suma mtsss yasake Jan wani tsaki yashige motarshi yayi gaba abunsa yabarta nan kasa zube ga kafarta daya taka har kumbarta ya sabule kefe ,

Abdallah yashigo gidan asaban mashin dinsa, har yayi parking yasauka kamar ance juya, yaga joda kwance, ya salam meyasame wannan yarinyar, ganin layin motar Ahmed yasa shi cewa "oh gosh "ita wannan yarinyar batasan nan gurin Dan iskan yaron nan bane,

I know shiyamata wani abu myb ma yataka ta da mota ne , ruwan dake hannunsa yadauko yazuba mata, bude idonta tayi tareda fashewa da kuka , Yace x ok2  meyasameka ne? tace bkomaie faduwa nayi

Abdallah yace amma dai koma ya ne kada kisake, bi wannan hanyar kinji koh, Ta daga kai, Yace gud yanzu ina yake miki ciyo ne, joda tace bakomai lfy lau nake, abdallah yace ok tashi kishi ga daga ciki,

 kasa tashi tayi se cije lebe take, idonsa yakai kan kafarta yace no wonder nasan zai iya wlh, kiyi hakuri kibarshi da allah kawai haka yarika hannunta har kofar dakinsu sannan yawuce side dinsu........

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 2鈨�9鈨�
Tin kan uniform har zuwa sauran littafan makarantar bawanda malam bai bawa hafsa yace tabawa joda,  hafsa abun duk yadaure mata kai aranta kuwa tace nasan abdallah ne akwai son taemakon jama'a, cike dajin dadin abun taje tasame joda takaimata uniform din joda kuwa se murna take tana fadan kai tufafin kyawawa ne , riga sawando ne red se hijab white, gakuma niqab black ,

Yau tin safe tashirya tayi wanka dama kuwa hafsa tagoge mata uniform dinta, jikinta har rawa yake tasaka uniform din,  hafsa tashigo tasameta tana famar yin kwalliya, hafsa tace kaddai naga kinyi wannan digen2 naki na hauka, joda ta tabe baki nifa idan banyi wannan kwalliyar ba se inga kamar nakode hafsa tace bakuwa zakiyi ba bani powder nan, tasha famata powder tareda pink lipstick, hafsa tace kam kungan ki kuwa gaki dakyau amma kina bata fuskarki da hauka

Joda tace ni wlh banga nayi kyau ba, fuska ta kamar anwanke Farin kyalle, hafsa ta kyalkyale da dariya tace to naji badai zakiyi wadda kike soba, yanzu zanje in shirya kafun nan kin karya , joda tace ke hava dai ba kisaka mun wannan bakin kyallen ba, hafsa Ohh. ..ni manga bani nan tinda ke komai bazaki dakanki ba gwanda ma ki koya tinyanzu bazan zauna zaman shirya ki ba kullum takarba tasaka mata sannan tawuce

Joda tagama shirin ta tsaf hadda wani aza bag kan kafasa Su joda an waye 馃槀 kofar parlour Su ta tsaya tanata kwalama hafsa kira, Ahmed dake gurin fridge zai dauko ma dad lemo duk haushi yacikashi wai wacece wannan tsaki yaja yawuce dakin dad , hafsa tafito tace to uwar Yan zanzana gani nafito, hafsa tace wai kinganki kuwa  kamar bulaliya bakauri ba kiba se tsawo kamar jimina,

joda tace to ai nafi wasu kuma ai kema duk gudanku dogaye ne jifa wannan yayan naki tsawonsa yakai na rakumi, hafsa  tace allah yasa yajiki wlh yafasa bakinki, joda tace nidai muje Dan allah gabana ma keta faduwa,, abdallah dake fitowa yace to ay seki dauko shi, Karasowa yayi kusanta yabude nikab din yarabb yafada wow whatapp veuryfull, hafsa tace bros kodai2 abdallah yace zanci ubanki wlh kodai me , Ahmed dayake kallon duk abunda suke yasauko fuskar nan ba annuri yace kewai Dan ubanki ban hanaki shigowa nanba ido tazare tayi bayan abdallah

Abdallah yace wai me wannan yarinyar ta tare maka ne inaruwanka da ita tinda ba akanka take saukaba, Ahmed yace zanfasa bakinka wlh nikake gayawa mgn, abdallah yace ke muje inyi drop dinku, Ahmed yace Hafsa wlh idan kika fita sena karyaki kinsan kuma zan iya, joda kam kasa motsi tayi still kuma idonta nakansa takasa daukesu ballantana tayi takanta, Ahmed yace mekinwani kafeni da mayun idonki, hawaye kadai kesintiri a idonta, Ahmed yace kobazaki fita bane, jus dinda ke hannunsa ya watsa mata a fuska gashi da shegen sanyi

Atake tarufe idonta hijab dinta duk yalalace yayi colour din lemon , ganin taki koda motsawa yakara fusata shi, yadunfarota kamar wani lion, yana kawowa gurinta yacabko wuyanta sezare ido, yake yace keeee wlh sena.......baikai karshen zancen ba yaga tana lumsashe idonta tana wani laudi kamar  taliya  sekuma tayi kasa bata kai kasaba saboda yaci kwalar hijab dinta dogon tsaki yaja yasaketa carab abdallah yacabketa tafada kansa, cike da takaici yace amma dai wlh Anyi marar imani nan gurin , yarinyar nan totally bata San ganinka muryar ka tamkar aradu yake agurinka amma kuma duk bai isheka ba seka hada mata da tsawa wlh watarana kashe ta zakayi

Hafsa dake gefe se kuka take, Ahmed yace kasan zan iya kasheta koh? Abdallah yace I know wlh nasan zaka iya, Ahmed yace so keep mouth, yajuya ga hafsa keko.....sekuma yafasa fadan zancen yakama hanyarshi, abdallah yace Hafsa bani ruwa plss,

Dasauri tadakko gorar ruwa aka watsa mata, dakuka ta tashi, abdallah shi yayi tabata baki akan abunda yake faruwa, hafsa tadakko mata wani hijab tasaka sannan tace kije bros abdallah yakaiki ni inazuwa, ba musu tabisa, cikin motama hakurin yake bata har suka isa skull yaje sujira hafsa tinda banisa , akafa hafsa tazo sannan yawuce sukuma suka shiga skull din............

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 3鈨�0鈨�
Seda yaga sun bace sannan Yakoma gida, hafsa taja hannun joda se office din headmaster, shi dakanshi ya gwada karatunta Alhamdulillah tanada irin nata kokarin sedai batada tajweed saboda haka aka bata aji biyu, har dai aka tashi makarantar jikinta bai saku ba tana tinanin hali irin na wannan mutum

suna shiga cikin gidan joda tabi hanyar dakinsu dasauri hafsa tariko ta, tayi narai2 da ido, tace Dan allah joda kada ki gayawa gwaggo abunda yafaru Dan allah wlh koni zai iya yiwa abunda yamiki fiyema, joda tace karki damu hafsa bakomai muke gayawa iyayenmu ba, wani lokacin mukan manta damuwa ko bacin ran dawani yasa kamu amma iyayenmu basu manta ba, hafsa tace nagode a kullum ina mamakin kaifin hankali irin naki

Joda tace bakomai nakoyi hakuri daga gurin baffana , na kuma samu kyakkyawar tarbiyar da har karshen rayuwa ta bazan yada ba, ina fatar ma infi hakan, hafsa tace allah yajikanshi ameen, hawaye suka gangaro afuskarta Dan kar ta saka hafsa kuka yasa tawuce abunta itama joda tagoge  idonta tashiga dakinsu

Har tabude kofar dakinta taji anjawota dakarfi, Ahmed ne yace ke Dan gidanku ni zaki cewa wai haka halina yake koke zanma haka? Meyasa kika ce karta gayawa uwarta zata rama mata ne Iye? Answer me, hafsa tace bakomai bros banason wani yaji haushin ka koya saka ka ranshi

Turata yayi dakarfi , tareda Jan hancinsa tsaki yace nafi bukatar wanda zaiji haushina akan wanda zai soni, nagaya miki bana bukatar ganin wannan yarinyar a parlour nan idan kuma nasake ganinta dake dakika kawota da itadin wlh duk sekun ji ajikinku ,

hafsa batace komai ba har yashige dakinsa, sannan tashiga nata kan kujera tazauna tana tunani Anya Ahmed Dan ummah ne da dad, Wata zuciyar tace dansu ne mana ay zaka iya haifuwar mutun baka haifi halinshi ba , allah kanunamun randa bros Ahmed zai gyara halayyarshi ameen

Abdallah yakasa sukuni , yarasa so" ko " sha'awa yake yimata, to inma sone mezai so ga village girl, inkuma sha'awa ce batada abun da zaisa aga sha'awar ta yanzu tafara boobs sedai akwai baya, to kodai small lips dinta ne kejanka, mtsss a'a idonta ne, kai aykoni manyan ido ne dani, to inaga dimple dinta ne, can kuma yace kai natina wlh gashinta yayi tsawon na ameesha phatal , hmmm kuji abdallah fah 馃憟馃徎 dole dai kadauki daya ko so ko sha'awa "

Amina ce rike da hannun saurayinta suna fira amota , Ahmed yashigo da motarshi yaje yayi yayi parking tuni tasaki hannunsa tace OMG, baby kaje gida wannan yayan nawa zai takura mun yanzu, wanda takira da baby yace akanme zanje gida sedai ko in kin gaji daganina ne, tace no wlh, Yace to sbd me zanje gida ba inda zanje idan zuciyar sojoji ne dashi nikuma ta kafirauna ce dani  ( wa'iya zu billah) a kullum murika kiyaye harshen mu daga alfasha ko abun ki

Ahmed yashiga gida abunsa tamkar baigansu ba , Wata ajiyar zuciya tayi , suka cigaba da soyewarsu, can ajima kadan Segashi, yafito yacanza kaya, bainufi ko ina ba se gurin Su, yana zuwa yasamesu manne da juna wai Su kiss suke , baiyi wata2 ba yashiga jibgarta ita har saurayin nata seda yaci ubansu dakyau sannan yace ke kunnen kashi ne dake ko? Kaikuma idan aurenta zakayi ina bukatar ganin iyayenka idan kuma ba aurenta zakayi ba, to wlh kada ka kuskura nasake ganinka akofar layin nan,

Yaron yataso se huci yake, yana fadan bari ganin kayi mana riske, wlh se in karya ka, Ahmed yazaro ido hava dai, yaron yace sosaima kuwa idan ka cika ka ajiye belt din ni bana fada da bulala, Ahmed wohoho wlh ina tausayin ka yoko ubanka ya isa yadunfareni balantana kai, ay nadakeka da belt shine sauki, Dan ina samaka hannu wlh zaka.......

Hannun rigarsa ya shiga kwashewa amina tace sayyid wlh kada ka hada jiki da shi zai kasheka abanza, sayyid yakara fusata yakuwa  yi cikin Ahmed, Ahmed Baiko motsa ba har yagama naushinsa Ahmed ko tangadawa baiyi ba, se abun yabashi tsoro Ahmed yace meyasa kake mamaki ne kagama, nan yamasa shegen naushi aciki tuni yadi kasa , Ahmed Au dasauri haka, hannu yadaga tuni sayyid yace plsss kar ka fidda mun yayan hanji 馃槀 Ahmed yace no its ollryt am leaving

Yamaida kallansa ga amina tuni tayanka aguje , yabita dai2 wata mota yahadu da joda kanta ba Dan kwalie Anyi mata kitso daya, dasauri tajuya yace Keee aykuwa ta tsaya bata juyo ba, yana isa gareta, yajanyo gashinta dakarfi, seda tayi kara mekike anan ne?

Batace komai bah jikinta serawa yake gashi yaki sakin kanta kuma da zafi, hawaye suka fara mata zuba , Yace wlh idan kina mun wani wai sunanki na qarya sena idaki, ni dodo ne koya, idonta arufe, har yagama yaturata kan amota yawuce, joda tadade tsaye ahaka sannan takoma dakinsu abunda zatayi ma seta fasa.......

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
    馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
       馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
         馃巹 馃巹 馃巹
            馃巹 馃巹
               馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 3鈨�1鈨�
Tin randa joda tafara fita islamiyya wani yasir yake damunsu haka zaiyi ta bibiyarta , tin hafsa na zaginsa har tagaji tasaka masa ido, Wata rana yakafe Su dole hafsa tabasu guri dai2 gate din gidan, Nan yagabatar mata dakansa , akan cewa shifa yana sonta so kuma da aure,

joda tace gaskiya ke bakida hankali yanxu ni zakisewa aure yaushe na iya tuwo bare nayi aure, yasir kuwa yadinga dariya, Yace ke baku dade nan garin bane? Naga har yanzu hausar ki se ahankali , joda tace bansaniba, yasir yace yihakuri ranki yadade

Ana haka se ga Ahmed yazo zai shiga gidan tin anesa yahangota yana mamakin yadda wannan tsular yarinyar ta isa tsayuwa da samari wlh kuwa watan cin ubanta yatsa ya, har zai fito kome yatuna sekuma yabasar, aransa yace ko gardi goma zasu cita agabana baruwana tinda ba hafsa ce ba ko amina,

Seda yakai dai2 Su sannan ya watsa musu ruwan cabi yashige gida abunsa tamkar baigansu ba, yasir yace amma dai wlh Anyi matsiyacin yaro nan gurin dubi fa yadda yalalace mana sutura, joda tace bakomai kayi hakuri baiganmu ba ne, yasir yace kamar ya baiganmu ba makoho ne shi koya? Joda tace to ai seka rama koh, yasir yace a'a yawuce, Nan yamata sallama yawuce,

Joda nashiga dakinsu gwaggo tace to joda zoki tayani fura zanyi yau nagaji da wannan cimakar, haka kuwa akayi suka zage dantse suka hada furar Su aka gyara nono aka zuba 馃構 haka masu aykin sukayi ta santin furar kamar me,

Joda tazuba ma hafsa a jug tabawa wata yar aiki takaimata, abdallah yafito daga dakin hjy shida amina yahango hafsa na shan fura, Yace iyyee hafsa ina kika samo kayan dadi? Hafsa tace wlh gwaggo tayi furar kamar ta ummah, abdallah yace hava dai , hafsa tace wlh fa bros akwai dadi, abdallah yace ok tashi ki karbo mun tawa hafsa ta ajiye cup din tafita aykuwa abdallah yadauko cup din yana sha baisan tym dinda ya shanye ba tass

Hafsa tashigo rike da plastic cike da fura, tace bros yau celebration na fura da nono 馃槅 abdallah yace nidai zoki zubamun , amina tace bros yanxu furar fulani zaka sha ' fulani ma na daji ne fa , abdallah yace wadannan sunada dffrnt ne basuda kazantar komai nagani da idona

Amina tace to nima asammin inji yadda take tana sha tafara woww wlh kamar furar ummah baqarya wlh hjy tafito tareda dad se wani manne masa take abunda Ahmed yatsana kenan yaga tana yiwa dad dinshi abu agaban su , dad yace bidirin me ake ne naga kun hadu haka, Hafsa tace dad fura muke sha zoka sha kar a barka abaya , Dad yace a'a nikam raben da nasha fura tin bayan rasuwar saratu Bankara shan fura ba duk wadda nasha bata min kamar tata

Abdallah yace to kuwa banda wannan kamar hannun ta yake, dad yace ar u sure, abdallah yace yes dad, dad yace idan najita badai2 ba zanmuki duka, sukace sun yarda Amina ce tazuba mishi hafsa takai masa


Yana kai bakinsa yace wonderful diz x a great, wlh sak hannun saratu, hjy najinsu tayi musu banza, dad yace wa yayi furar haka, hafsa tace dad masu aikin da aka dauka ne last time, dad yace dz gud to ina son ganin wannan bafulatana domin ina son cimakar Su, hafsa tace to dad se randa kake free koh? Dad yace se 2morrow hafsa

Sallama sukaji anyi daga waje, tsalle amina tadaka antyba2 wlcm, hjy tace Oyoyo big sister, mansura tayi ma kanta guri tazauna , tagaida dad ya karba bayabo ba fallasa, hafsa tace barka da zuwa anty

Mansura ta ballamata harara, kamar batajiba , dad dake kule dasu yace zonan Hafsa yajata sukayi dakishi Mansura tace yo naji iskanci wannan fa bayarshi ceba, hjy tace Uhm haka yake banbanci yake nunawa kiri2

Mansura tace to ai laifinki ne anty kizo mukaishi gurin mai kwalshi aikinshi kamar yankan wuka ne , hjy tace kenifa nagaji da barnar kudina abanza aiki baya kyau Mansura tace tab wlh wannan ba kuskure, ana haka Sega Ahmed yashigo ko kallan inda suke baiyi ba yanufi kofar dakinshi hjy tace Ahmed........yatsa ya cak batareda yajuyo ba, tace bakagan mansura ba halan? Dogon Tsaki yaja yawuce dakin sa.........

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 3鈨�2鈨�
Mansura tace amma dai wlh so wawa ne inba hakaba ya za'ayi nmj yamun haka anty dubi yadda ake mun rushing amma ni duk duniya wlh banga namijin danakeso kamar Ahmed ba, abdallah yace yo naga maita  tinda baya sanki ay seki kama gabanki ko nibanga abun so acikin Ahmed ba wlh indan saboda kyan sa ne, Tokuwa kisani kyan Dan maciji ne, gabansa fari bayan sa baqi

Kina auren Ahmed ina gayamiki kin gama yawo, hjy tace kai ya isa shasha ba uwarka ceba kawani tsayawa kana bata mgn haka, amina tace wlh da gaskiyar bros, anty surah idan idan kika aure bros Ahmed wlh kashin ki yabushe, to waima taya zai aureki bayan ko tantance fuskar ki baya yi

Hjy tace bawani nan fuskar kowa yasani iskanci ne kawai,  mansura tace nidai anty kona hakura dashi kawai kada naje nadawo se zanbaga ma malan kudi nake amma har yanzu ba labari kuma da alama wannan yaron bazai canza ba

Hjy tace dubi ke Dan allah watsamana plan zakiyi? Mansura tace ohh. ..... namanta ne sam wlh, hjy tace iyye wato so ya rufe miki ido to wlh tin wuri kisake tunani abunda muka tsara shi zakiyi ba soyy ba kada kije kimanta shaukin so yadebeki , hakarmu takasa cimma ruwa

Mansura tadafa hjy tace karki damu antyna komai zai tafi yadda ki keso baxan baki kunya ba kinfi kowa sanin waye ni, abdallah yaja tsaki yace duk dukiyar da allah yamuku bata ishekuba sekun kara da kwadayi, hjy tace me kuka cemaka zamuyi da iskancin ka abdallah yace mama niba yaro bane kuma nasan abunda nake, ko Dan primary yaji firar ku zai iya fassara ta balanta mai masters

Hjy tace amina kema wai kin fassara  Amin ta kyalkyale da dariya hava mamana namiji ma yafahimci firar ku balantana ni mace , hjy tace to wlh ku kama bakinku banason jin wani zancen, karku sake zanjen nan nasake jinsa kunan ta dashi kwata2

Abdallah yata be baki yace whatever dai you shall remember Ahmed x solider, bazaku iya hada masa tuggu ba, sannan kwan wayo ne nagaske ko hanjin mutun yana gani, Ahmed zai iya kamaka yamaida laifi akanka tahanyar dakuke son bi,  hjy tace munji dai jeka2 mungode da tunarwa,

Abdallah yayi murmushi yace anty surah idan kika nace kan auren Ahmed wlh am telling you, u will on dy n regretting, so u hv to take a hrt, hjy tace kai bamusan iskancin banza ina ruwanka, abdallah yace mamma lamme tell her my point. hjy tace kai kabace mun dagani nace, abdallah yace ollryt am leaving, hjy tarakashi da harara 

Mansura tace anty aduba zancen abdallah fah! hjy tace idan zaki dinga biyewa zancen sa zai karya miki da zuciya, kada kiyarda ke macece kinfi kowa sanin namiji yaro ne duk yadda kikayi dashi haka xaibi , mansura tace anty ban katsekiba taya kenan?hjy ta harareta tace kidauki hankalinsa mana tahanyar shiga jikinsa duk yadda kika San kinsaba haka zakiyi masa

Mansura tace ohh.....antyna ay banfahimceki bane daga farko se yanzu, to ai anty kuma kinsan shi ko kallan mace bayayi bansan tayadda zan bullo masaba, hjy tace ke kizama mutun ayi mgn dake hava Dan allah, dubeki gafari gakyau kinada komai da namiji yake buqata diri se Wanda yagani boobs gasunan kamar zasuyi magana, mansura tace kai antyna, kuma boobs dinfa sunsha mouth din guys amma ko kadan sunki zubewa, hjy ta zungureta ke dallah yimana shiru,

Yanzu bazama zakiyi ba kitashi kishiga dakinsa kifara aiki, mansura kam wlh anty kwarjininsa yayi yawa har bana iya hada ido dashi, hjy tace to wlh kuwa dasake dole kicire tsoronsa zanyi wani abu akai, mansura tadauko wani tirare tadaka, takalli hjy sukayiwa juna murmushi sannan ta dunfari dakin Ahmed..........

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 3鈨�3鈨�
Tana isa tamurda kofar takuwa yi sa'a kofar abude take, da sallamarta tashiga ciki, bata samesaba gabanta se bugawa yake, kan kujera tazauna, tana karewa hadadden dakin kallo, se kamshi kakeji kala2, kofar toilet aka murda hakan yadawo da ita daga duniyar tunani , Ahmed kuwa baikula da mutun ba daga shi se towel iya cinyarshi, shafe jikinsa yayi sannan yafesa body spray kamar zai kare gwangwanin, sannan yashiga  shafa mai , haka yake bin jikinsa kaba2 yana shafa masa mai sannan yadauko cum yataje sumarshi, kamahin mansa kadai da sabulunsa yasakata cikin wani yanayi

Yawunta tashiga hadiya lokacin datake karewa surarsa kallo, farine dogo Mai faffadan kirji jikinsa duk gashine Wanda yake kwance luf, duk gabobin jikinsa dogaye ne , idonta takai kan hancinsa dayake dogo tamkar na hrithic roshan , se manyan idonsa, ga eyelashes dinsa zara2 kamar namace, girarshi kuwa haka take kwance maiyawa da ita , lips dinshi takuarawa ido gasu pink sosai gasu very small , sajensa luf kan fuskarshi , aranta tace ance Dan Adam baicika goma ba Tokuwa yau naga 12 ma ba ten ba domin Ahmed ba abunda yaragu dashi kyau dukiya ilimi, ni kuwa asea nace me ake da hali irin nashi mutun kullum kirarshi ahade yana shan nagani

towel din yake kokarin cirewa har yaxare daurin,  kamar ance duba, yaga mace acikin mirror takafesa da ido se murmushi take , ohh..shiit yafada tareda sauri yamaida daurin , wani karamun blanket yadauko yayi rufa dashi yaxuyo afusace, kee mekikeyi adakina? Mansura ta taso cikin wani tako ta iso gareshi, Seda taxo daf dashi sannan tace hava my Ahmed kasanfa ina sonka meyasa kake son bani wahala ne, Ahmed yacije lebe yanunata da yatsa yace kinsan duniya babu abunda natsana sama da ace ana sona da cewa kikayi kinfi kowa tsanata toda zakifi burgeni, mansura kuwa taji haushin kalamansa

kwalarshi taciyo tace Ahmed look at me look into my eyes, babu namijin danakeso aduniya sama dakai wlh Ahmed ina sonka fiyeda yadda nakeson kaina, Ahmed yawanke ta damari Seda taga wata wuta, Yace nizaki ciwa kwala, agabana kike fadan wai Kina sona, to wlh ina gargadinki ki fita daga rayuwata, inbahaka ba wlh senasa kinyi nadamar zuwanki duniya , yahankada get out marasa kunyar yarinya komata sunkare aduniya Kina tunanin zan so kine, wawiya jahila

Ya isheka Ahmed bari ganin ina sanka kanemi gayamin magana, Ahmed yace ohh to ay seki rama, hawayenta tagoge tace wlh Ahmed baxan taba dena sanka ba har abada kuma wlh sena aureka zaka shigo hannu, Ahmed yajuya yacigaba da shirinsa tamkar baisan da mutun adakin ba, dole dai dataga zaman baiyi tafito cike da kunci tanajin haushin kanta

Tsaki yaja yace mezanyi da wadda takusa zuwa age dina, wayarshi yadauko ya duba, 5miss call  daga Mahmud,  kiranshi yayi kamar zata tsinke sannan yadaga, Mahmud yace wai ina ka shiga ne inata call dinka , Ahmed yace ina toilet ne, menene schedule a yau ? Mahmud yace sekazo zakagan, Ahmed yace please kazo kadaukeni, Mahmud yace kaikuma fa sekayi me? Ahmed yace inzaka zo in kuma baxaka zoba shikenan, Mahmud yace aikuwa bazan zoba, Ahmed yace idan kazo bakamunba wlh

Tsab ya gama shirinsa yatada sallah azahar, sannan yabi lafiyar gado har yasoma bacci can yaji ring din wayarshi yadamesa  tsaki yaja yakara shigewa bargo can kuma tasake ruri, dolensa yagada baima duba Wanda yake calling dinba, jin muryar commissioner yasashi tashi zaune, Yace Ahmed bakaji Kirana bane?Ahmed yace sorry sir " ina bacci ne, cmsner yace Mahmud baigayamaka ina nemanku ba?Ahmed yace ni baigayan komai ba, cmsner yace ollryt kuzo yanzu ba atare ina nemanku, Ahmed yace sir seyanxu2 kake buqata cos wlh bacci nakeji, cmsner aranshi yace inbanda kokarin yaronnan da davaru wlh dayanzu ya'ajiye aikinshi, cmsner yace yes yanzu nake nemanku bana bukatar sake nemanku, Ahmed yaja tsaki ya tsinke wayar yakoma kan gadonshi yacigaba da baccinsa

Hafsa tasame gwaggo taga yamata yanda sukayi da su dad, gwaggo tace bkomai ay aykinmune zanrika masa kullum hafsa tace yauwa gwaggo na wlh da dadi, gwaggo tamata  dariya, yau harda danbun gero zanmuku, hafsa tace lah gwaggo Kin iya, gwaggo tace idan anyi zakigani hafsatu , hafsa tace to kiyi dayawa saboda kowa yanaso, gwaggo tace karma kidami kanki yanxu zantashi  ba'afi awa biyuba gida yadau shegen kamshi ko ina jinsa kake, hjy tin asama takejin kamahin, tadauko taga me ake haka abun haushi taga gwaggo a kitchen tana kwashewa, tabuga tsaki , tace ke tsabar gidanku ce dazakiyi mana barnarta haka kiyi fura kiyi danbu

Gwaggo tace kiyi hakuri ranki yadade, hafsatu ce tace maigidan na buqata daku gabadaya, hjy tace ubanwa zaici muku wannan kazantar, dallah kifice mun dagani kafin inyi ball da abincin, gwaggo taraba tawuce, dai2 nan Ahmed yafito ganin hjy tarike kugu yasan rashin mutunci tashukawa gwaggo , baice dasu komai ba, yashige dakinsa can yaji hjy na zage2, hayaniyar ta tahanasa sakat yafito rike da new paper, Yace wai lfy kuka cikamana gida da hayaniya, ganin hafsa na hawaye yasa shi yin shiru

Gurinta yaje yaduka 6 lfy me akayi miki, tace bros dad ne yace yanason furar gwaggo shine tamasa kuma naga zatayi danbun gero senace tayi dayawa saboda nasan kunasansa nan gidan shine, hjy tabarar duka kuma tayita zagin gwaggo

Hannunsa taja bros zokaga danbun kitchen sukaje yaga danbun a kasa yasha vegetables da hanji, kamshinsa kadai yatabbatar masa yayi dadi , se idonsa yakai gun fura lumui2 da ita

Yajuyo yakalli hjy daketa kada kafa yadanna bell din gidan segamasu aykin duka yakallesu daya bayan daya, Yace kada naga Wanda yagirka koda indomei ce, hjy tace to idan ba ayi abincin ba mekakeso muci? Ahmed yace kuci Wanda kuka barar ay ba'a banza muke nemaba, hjy tace to kai kake neman kudin da ranen sense. Ahmed yace kai kutashi , kundai jini da kyau wlh duk Wanda yagirka ko ruwan tea bakin aykinsa kuma wlh baxai karbi salary din wannan month ba

Yakalli hafsa yace zeki kwashe danbun kifito da furar Seda ta gyara kitchen kamar ba ayi komai ba sannan yasakawa kitchen key yawuce abunsa , hjy tace billahillazi senayi maganin wannan yaron bayadda zai rika juyamu yadda yaga dama...........

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
    馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
       馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
          馃巹 馃巹 馃巹
             馃巹 馃巹
                馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 3鈨�4鈨�
Hjy zaune agaban dad tana korafi kan Ahmed, dad yace wai ke yanzu dakika tasani agaba mekike son inyi masa ne dukansa zanyi kome, hjy tace bazancen duka bane, kawai kai kake dagidanka order kai muke gabadaya nmj har shi, nagaji da wannan zaman dole kowa yadauki matsayinsa, dad yace idan nafahimceki sokike kizama boss agidannan fada yadawo kanki umarni da order right? hjy tace eh to nidai baikamata ace ina matsayin uwa agaresa ba amma baya dauka ta da daraja baya bin umarnina, sannan ni ban isa Ince ayi ayiba ko nahana yahanu a'a dole sena rika bun umarninsa, why?

Dad yace to hakuri dai zakiyi Ahmed koni karan kaina ban isa in sakashi dole ba yanada wata irin zuciya ne nibansan inda yagado taba, hjy tace shikenan zandau mataki da hannuna idan har kai kaka sa kwatarmun hakkina , dad yace fyn gaki ga hanya kindai sansa farin sani, tin farko dakin daukesa uwa shida kan warship ay da bai rainakiba, hjy taja tsaki tabarmasa room dinsa, cike da takaici, aranta kuwa tadauki aniyar ganin bayan Ahmed koda kuwa zata rasa duk wani abu data mallaka, toh fah "

Mahmud kwance kan gadon Ahmed yace wato mod ko wlh tin randa muka bar dajin nan nake cike da kwadayin fura bantaba shan furar datayi dadin wannan ba tin bayan ta ummah, Ahmed yace toni me zanmaka ne? Mahmud yace I don't know Dan iska kai goma ba'a zancen kirki dakai, Ahmed yace tona tanbiyeka ne? Mahmud yace nafa fika iskanci wlh, Ahmed ohh.....hava dae, Mahmud yagalla masa harara yagyra kwanciyarshi, Ahmed kuwa yadauko system dinshi yana dubawa ,

Hafsa nagani aguje  se haki take tayi dakin dad, ko sallama batayiba tafada dakin sa. yadago kai yana kallan ta yace hafsa lfy naganki haka? Se shesheka take tace dad joda ce ba lfy wlh gatacan se murde2 take cikin ta ke ciyo kamar zata mutu, dad yace Subhanallah, Ahmed nagida? Hafsa tace ehh yana daga ciki, dad yace jekice yazo ya duba ta, hafsa tace wlh dad bazai dubata ba, sedai ko in kai zakamasa mgn, dad yace shikenan jeki zanmar waya, haka kuwa akayi yasaka kiran Ahmed

Ring daya yadaga tareda fadan yes dad, dad yace Ahmed kana inane yanxu, Ahmed yace am in home, dad yace gud, Ahmed kaje kaduba wannan fulanin da aka dauka ayki ance wai yarinyar ba lfy katacan ciyon ciki ne, Ahmed yace what dad, nizan dubata yanxun gsky ina ayki ne buh akira driver da hafsa sukaita hospital, dad yace hakan dakayi aganinka ka kyauta kenan Ahmed yace bahakaba dad inada ayki dayawa agabana so kuma ni.....Di. ....Di yaji wayar ta tsinke, tsaki yaja kawai saboda anrenan wayo nizanje induba ta, nikadaine doct agari ay wlh gwanda narasa komai akan nataba wannan najasar

Mahmud yabuga masa dogon tsaki yace in angirma asan angirma, Ahmed yace da buhun uba dawa kake, Mahmud yace kaidin wani abun zakayi ne, Ahmed yace kabarmun dakina kafin muyi kaca2 dakai, Mahmud yace ay kobaka fadaba nasan dakinka ne buh baxan fita ba kazo kafidda ni, Ahmed yaja tsaki yadauko rigarsa yasaka yace aysekayita zaman, yafice yabar dakin

Hafsa tajasu se wata hadaddar hospital, suna isa wani nurse yazo da kujera suka axata, hafsa tace ina doct inmasa bayanin abunda kedamunta nurse din yace base kinga doc ba yana dubata zai gane matsalar, hafsa tace amma dama kunsan dazuwanmu ne, nurse din yakalleta yayi murmushi yacigaba da tafiya, sama yayi da ita gwaggo da hafsa suka rufa masa baya, room no 7 suka shiga da ita, bayan kamar minti goma yafito daga dakin yace doct na bukatar ganin mahaifiyar wannan yarinyar, den kuma dakinje kifara masa bayani kawai doct din yana da matsala idan kikaga ya dubi kofa to yana nufin shikenan zaki iya fitowa, hafsa tace shikuwa wannan wani irin doct ne haka dayake da regulations, nurse din yace haka rules dinshi suke baya mgn a lokacin dayake duba patients

Gwaggo tace bari inje hafsa , sallama tayi tashiga dakin sa a tsaye ta samesa yana kokarin sakama joda drip kujera yaturamata tazauna sannan shima yakoma mazauninsa, fuskarshi sanye da glass fari gakuma face mask, hannu yamata alama dashi akan taci gaba da basa bayani

Gwaggo tace likita tun daren jiya takecemun kafafunta naciyo da cikinta kuma setakejin kasala sosae ajikinta doct yagyada kai yafara rubutu , tacigaba sekuma yau tawayi gari da tsara se murde2 take doct yadakatash sheta da a hannu alamun ya isa kofa yanunamata gwaggo tafito nurse din yashiga...........

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 3鈨�5鈨�
Doct din yacema nurse din nasakamata drip saboda tawahala den jeka dauko mun pad da pant, ka ajiye mata kan gadon tana farkawa ka kirani, haka kuwa akayi nurse yazauna zaman jiran tashinta doct din yafito, hafsa tabisa tana doct meke damunta ne ? doct yagada mata hannu alamar yana zuwa file din dake hannunsa yabata, yawuce abunsa,

Hafsa nadubawa tace toh fah " gwaggo kinga al'ada ce tafara, gwaggo tace amma ay damun sani dabamu zoba se ayaga tsumma tasaka shikenan , hafsa tace ay gwara damuka zo domin kinga yaxomata da gardama , kuma ay andena saka tsumma a yanzu sedai pad, gwaggo tace komenene pad kuma ganin doct na sauri yasa suka rakashi da ido ,

Dasauri yashiga tareda rufo kofar, nurse yagani rike da ita se kucce2 take tsawa yadaka mata kee ki mana shiru tuni takoma kan gado talafe gashi duk tabata gadon, doct yace ungo wannan zaki iya shiga wannan toilet kigyara kanki akwai ruwan zafi , ahankali tace nifa wani abu yajimun ciyo gurin fitsari na jini kefita, doct yace kije kiyi wanka zan miki bayani kinji kanwata, tace bazan iya tashiba doct, likita  yace nurse bamu guri toilet yakai ta yasata cikin baho wanka wata ajiyar zuciya tayi, Yace yade tace da dadi wlh, likita yace to kiyi wanka, joda tayi narai2 da ido likita yace menene kanwata tace bakomai kafita mana kuma banda wasu tufafi, Yace tobari ayi mgn sukawo miki

Bell yadanna, Sega nurse yazo yamasa bayanin abunda ake buqata, shima ya yiwa su gwaggo bayani bajimawa hafsa takawo mata wata atamfa riga da skit, dae2 nan kuwa tafito wanka lulube cikin katon towel doct yace ke ki kuma ciki mana akawo miki kayan, Seda tasaka tafito sannan tace nifa jinin bai dena zuba ba, likita yace tobaki saka pad din bane? tace nibansan ya a keyi ba

Karbar pad din yayi yalaka akan pant din yace kinga yadda nayi to haka ake jeki saka ba musu taja tasaka, taxo tazauna , Yace wannan jinin haila ne kika fara every month zakiyi daga kwana daya zuwa shabiyar, haka dae yamata bayanin komai

Joda tace nikam menene every month, likita yayi murmushi yace bakije skull bane, joda tayi shiru, yasake cewa bakije makaranta bane, joda tace bana boko islamiyya kawai nakeyi , Yace to meyasa bakiyi, joda tace babana yarasu ayki muke gidansu wannan yarinyar datakawo ni , likita yace a ina kike a hadda tace yanzu nafara mu fulanin daji ne, Nan likita yanemi sanin labarinta bamusu tamasa bayanin komai har zuwa yanxu

Yace to nikam wannan ya Ahmed din sonsa kike ne koya, tace kam wlh karkasa yakasheni ni wlh natsanesa arayuwata tinda naga baya sona, likita yace taya kika San baya sanki, joda tace kaiwai bakaji yanda yake dizgani bane, likita yace toke meyasa kike tsoronsa dayawa haka, joda tace nima bansaniba, likita yace tym natafiya naso nabaki somes advice akan wannan guy , ga wannan magungunan dazaki rika Shane tayi godiya tafita yabita har waje yayi gyaran murya yace kikulamun da kanki plss kirika shan magani akan kaida inba hakaba, zaki jawa kanki problems dayawa, murmushi tamasa nagode likita mai kirki

Haka suka dawo gida dukda bawani kwari  takejiba , hafsa kuwa senan nan take da ita, se kusan magrib sannan takoma side dinsu,  sallah tayi tukun tafara cin abunci sannan tayi wanka tashiga bacci abunta, joda kuwa mararta talafa mata tasamu itama tayi bacci cike da mafarkin likitanta mai murmushi  , tace wannan haka nakejinsa tamkar ya Mahmud shima haka yake cemun qanwata, ya allah kahadani da Mahmud ko a ina ne, ni kuwa nace shakurumunki joda, indai kere na yawo zabo na yawo to dole watarana zasu hadu

Koda akayi  12 joda tajita latsama acikin jini haka tasaka kuka tana kiran gwaggo, gwaggo nabacci taji kukan joda, tasowa tayi tana tanbayar lfy joda tanuna mata jikinta, gwaggo tace tokekuma naki yanayi haka yake Muje bayi nagyaraki , haka gwaggo tajata sukaje toilet tawanke mata jikinta , sannan tasake bata wani pad talaka , aka canza kyallen katifar............

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 3鈨�6鈨�
Kwananta  biyar sannan tasamu tsarki, ranar lahadi takoma islamiyya ,sun dawo se sauri take yunwa ta I sheta kamar me, hafsa nata yi mata tsiya, sunkawo cikin harabar gidan taji wata murya dabaxata taba mantawa ba, yana cewa plss mod kayi sauri,  jakar hanunta tayada, taje aguje bayan motar ta samesa kansa a kasa yana daure talkaminsa,

Anatse tace ya Mahmud ga fura, 馃槄 dago kansa yayi dakarfi yana joda kece ina kika shiga naje dajinku bansameki ba, ya akai kikazo nan gidan naganki da uniform fin nurul kharim koday har kinzama yar abuja ina gwaggo da baffa

Ahmed  yaja tsaki kai bani key din motar zan wuce, bansan iskanci, Mahmud yace Ahmed wannan sune wadanda aka nuna gidansu a TV Wanda akace akwai fetur, Ahmed garesu ne nakeshan fura a dajin , Ahmed yace towai natanbiyeka ne, dallah kabani key zanwuce, Mahmud baiko sauraresa ba yacigaba da tanbiyar joda tace ay baffa yacika, innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, allah yajikansa fita yayi yabar Ahmed suka shiga ciki domin ganawa da gwaggo, Ahmed yace wato ni yamaidani Dan iska akan wannan shegiyar

 tsaki yaja sannan yatada motar, joda dagudu tashiga dakinsu, tana gwaggo zoga ya Mahmud, dakinsu yashiga yasame gwaggo na karatun qur'an Mahmud yazauna joda kuwa tafita takawo masa ruwa, gwaggo takai aya yajuyo cike da farin cikin ganin Mahmud tace yo wanake gani haka, Mahmud yace gwaggo nine dama nan gidan kuke dazama, gwaggo tace Mahmud labari ne maitsayi, Yace gwaggo ashe baffa yacika gwaggo tace ka gani dae Mahmud, Yace to allah yagafarta yakyautata makwancinsa ameen,

Mahmud yace ay bansan kunanan gidan ba kullum ina ciki, Ahmed babban aboki nane atare muka taso , atare muka je dajinku shidae yanada kyankyami shi isa bakya ganinsa, gwaggo tace ay base kamana bayanin saba munsan komai akansa, Mahmud yace Ince  dae baimuku rashin kunya ba

Gwaggo tace a'a ay shi haka yake kamar baya ganin mutun baruwansa da sha'anin mutun matar gidan ce dae wlh gata nan, Mahmud yace haka fah suke sea hakuri kawai, gwaggo tace yo mu ay bama shiga sha a ninsu kaga hafsatu itake sonmu wlh ta taemakemu sosae arayuwanta , Mahmud yace zata iya itafa batadauki rayuwa da girma ba, gwaggo tace haka ne fah sedae fatan dacewa

yinin ranar Mahmud dakinsu ya yini gwaggo nabasa labarin su, Yace insha Allah zai binciko musu kudinsu, gwaggo tamasa fura, yasha se santin furar yake, hafsa ma tadiba takaima su abdallah da dad, dad yace yana buqatar furar a kullum da kuma irin danbun geron da gwaggo tamasa kwanan baya, haka kuwa akayi gwaggo takoma mai aykin dad dukda ko afuska baitaba ganin taba amma yana musu alheri sosae , duk wani abuncinsa yakoma hannunta, haka takemasa duk abunda ya buqata hafsa tajera masa kan dining kida dae rana ba'a taba samun mistake ba sabanin sauran masu aykin dazaiji girkin yayi yaji kokuma ancika mai dayawa............

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
    馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
        馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
           馃巹 馃巹 馃巹
              馃巹 馃巹
                 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 3鈨�7鈨�
Yaune su hafsa zasu yi jararrabawar karshe kuma Yaune iyayen yara zasu hallara a  makarantar , domin ganin yadda karatun yayansu yake tafiya,  karfe 2 aka fara gudanarda taron da dae ake kiransu suna bada karansu kuma ana musu tanbaya, haka har a kazo ga hafsa inda ta uraemic Mahmud ido takasa yin komai Seda taga Ahmed nabinta da harara sannan tashiga taetayinta, harkuwa tacinye lokacin ta kadan yarage balaifi ba'a mata gyara sosae ba dukda haka kuwa Ahmed baiyaba da qoqararinta ba,

Su joda aka kira domin su waqar da aka basu kusan su 5 joda ce mai rera waqar sekuma yan amshinta su 4, cike da kunya tafito filin tafara gabatarda waqar, cikin wata zaqakkar murya ke kyace balarabiya ce ke rera waqar nan , Ahmed yayi shiru yana saurarenta har taxo karshe sannan suka rufe da addua, guraren 6 aka watse joda kam tasha kyauta kamar me, allah kaday yasan iya adadin mazan dasuka koma gida da zakakkar muryar joda aransu

Acikin kyautar hadda Wanda yabada 50k ten 5 gasunan dae, Mahmud kuwa duk murna tacikashi, suka dawo gida kowace danata kyautar, suna isa taruga aguje gurin gwaggo tana murna, gwaggo tace nidea kada ki karyani Dan allah nan tazubewa gwaggo kudin da sauran littafan data samu, Mahmud yashigo yasamu gu yazauna, Yace aifa yau bakin yr fillo baya rufuwa, joda tace nifa banasan tsokana, Mahmud yace au wato ni nake tsokanarki koh? Joda tace a'a banceba ya

Mahmud yace ni kuwa gwaggo inba damuwa mezaihana kisaka joda a skull ne, gwaggo tace badae bokoba gurin yahudawa akoyamata miyagun dabi'u Mahmud yace ba abunda za'a ko yamata se dae2  kinga yanxu rayuwa bata tafiya yadda kakeso sekana Dan bokon nan koda or level ce tana amfani yanxu baga hafsa ba ay college take amma aybakiga hallayyarta ya canza ba muma kuma gamunan, joda tace nikuwa da likita zan karanta saboda nawarkar da cutar data kashe mun baffa na, Mahmud yace kiwarkar kodai kibada naki gudummawa, joda tace ehh ay shine abunda nake nufi,

Gwaggo tace tonidae senayi istihara akai naga yayadace, ayi idan alhkairi ne allah yatabbatar mana dashi idan kuma sabanin hakan ne saemu hakura , Mahmud yace insha Allah ma alhkairi ne agaremu , joda tace kai gwaggo sekinyi wani istihara, gwaggo tace yomekike son inyi bayan ita neman zabin Allah nefa, joda tace to Allah zabamana mafi alkairi ameen

Mahmud yasame Ahmed kan zancen yana son saka joda skull wace yake ganin tadace asakata, Ahmed yace to waini ina ruwana da itane baruwana da duk abunda yashafeta kajiko kada kasakemun zancenta banaso, Mahmud yace to itakuma meta kashe maka, Ahmed yace nace maka bansan zancen ko dole ne hava, Mahmud yatabe baki Allah yashiryeka da wannan bakin halin, Ahmed afusace yace mutum nawa nakashe dazaka wani cewa bakin hali, Mahmud yace yo Ai gwanda wanda yakashe mutun idan akan kuskure yayi idan yatuba akanka

Ahmed yayi kadi da turaren dake hannunsa yayi cikin Ahmed yacabko wuyansa, idon nan sunyi jajir dasu, Mahmud yace wow shi isa nake sonka akwai zuciya kamar zaki, Ahmed yaqara matsesa da bango se huci yake tamkar wani maciji, Mahmud yakwace rigarsa dakarfi yatura Ahmed kan gado, yanufi fridge yadauko masa eviron drink, yamika masa Ahmed yawulgashi kasa yacigaba da kallon kafafunsa yana ajiyar zuciya, Mahmud yadafasa yace relax man, Ahmed yajanye hannunsa , dole Mahmud yabar masa dakinsa, yanufi dakin gwaggo

Mahmud yace gwaggo ya kin amunce zancen karatun, gwaggo tace toni dae ba abunda zance sedai allah yasanya alkairi yasa alhkairi ne, Mahmud yace to mungode gwaggo bari muga yaushe yakamata mufara apply din makarantar..........

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 3鈨�8鈨�
Mahmud yasame hafsa sun tattauna kan zancen karatun joda, hafsa tayi matukar murna, Mahmud yace yanxu se karshen zango kenan kafin nan ma akwai wani mission da za'a turamu, hafsa tace to ya sekun dawo allah yadawo mun dakai lfy, Mahmud yace iye mekika ce?  hafsa tace no...eh. ...dama cewa nayi allah yadawo muna daku lfy, Mahmud yayi murmushi yace ameen 6ter

Yau takama Friday  Yaune ranar da su Ahmed zasuje  yola state , tsaf suka shirya sukayi bankwana da kowa Ahmed yace hafsa inagayamiki duk shegen daya shuka miki rashin kunya to wlh kimun waya, hafsa tayi murmushi tace bakomai yaya komai zaitafi dae2 insha Allah, gud semun dawo, har mota tarakasu se satar kallon Mahmud take wanda baikosan tanayi ba, bayan sunwuce da kwana daya Sega wani David yazo akan maigidansa yaturosa zairika yiwa joda lesson kafun sudawo, ba bata lokaci yafara yiwa joda lesson kullum bafashi, idan tagama lesson takoma gun hafsa takara koyamata  ABCD suka fara, dayake bashida hausa, hafsa ke ko yamata hausa, haka zatayi ta masa zancen kurame idan bata gane ba,  cikin sati ukku tafara ganewa, har anfara da party of speech,  tin kan noun har zuwa karsehensu, kafun kace ha, Sega joda ana turanci, maths kuwa ta iyashi sosae ba'a barinta abaya dama takware agurin lissafi ,

Daganan kuma se aka fara subjects, na primary, intro technology, P.H.E, science, social studies, cumputer etc, suma dayake ba wuya nan danan tagane, haka abun ketafiya, har zuwa wani Dan lokaci sannan akafara, na secondary skull,  kafun su Ahmed sudawo joda komai fyn, turanci take bakama hannun yaro , abun se yayi tabata mamaki wai yau it ace kejin yaren yahudu

Soyy takullu maikarfi tsakaninta da yasir domin kuwa yasir akwai kyawawan hali gakuma girmama naga ba,  gwaggo har tasan dashi sun aje zance akan cewa za'a yi mgn idan yakarkare aykinsa a suleja, hakan yamasa dadi shima kuwa yana karawa joda haske akaratunta ita kanta batasan tanada wannan ilimin ba seyanxu, hafsa ma abun namata dadi hadda ma ba'a barta abayaba, haka take yin abunta cike da haqaza

Ahmed haushi yacikasa, yadubi Mahmud yaxasuyi mana haka mun aje akan wata biyu da sati ukku zamu bar garinnan yaxasu sabamana alkawari su sake bamu wani aykin daban, Mahmud yace hakuri zamuyi nikaina inada important issue wlh, to ya zamuyi allah yasa hakan alkairi ne agaremu ameen

David yacewa joda tashirya on Monday zasuje turkish intentional skull, acan akamata gwa akaga tawuce zama primary, secondary ma ko ss zataje, kasancewar batada, primary certificate ne aka bata jss3, murna gun devid ba'a magana koba komai oga zai ji dadi, joda ma haka itada hafsa sunyi matukar murna da hakan,

Ran Friday aka gama komai nxt mndy tafara zuwa, skull cike dakunyar uniform din riga da skit ne iya gwaiwa yake se hula, haushinta daya gashinta dabaya shiga acikin hular , hafsa tace kifara retouching dinshi zairage yawa , joda tace kenifa ba yanxu ba segaba,  zan rika sakamasa vatika dole zai kwanta , hafsa tace kyaji dashi ,

Joda batada kawa kodaya, ita kadai ke karatunta, dukda akwai maza amma baruwata dakowa, dukda kuwa anason kawo mata hari amma ba'a ga fuska ba, karatun ta kawai tasa agaba, malamai namatukar alfahari da ita, hujjar joda nakin kula kowa shine, ganin duk makarantar daga yayan ministers se prop itakuwa bayar kowaba mezaikaita kawance dasu

Sati biyu da fara zuwan joda skull, Yaune kuma su Ahmed zasu dawo, batareda kowa yasan da zuwansu ba, hafsa kuwa tanata kokarin zuwa skull dinta a saudia tazabe zuwa karatu, joda se korafi take akan hafsa zataje tabarta, ranarda zataje aranar su Ahmed suka dawo , dole tafasa tata tafiyar se bayan 2dyz,

Mahmud sashin gwaggo ya yada zango yana shiga yabuda fridge yaga kuwa da akwai Yar gidansa, yawashe baki yadauko yazuba a cup yafara sha, joda tafito kenan daga wanka daga ita se zani, ita bata ganshi ba tafara shafe shafenta, Mahmud kuwa rudewa yayi ganin irin kyakkawar surarta............

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 3鈨�9鈨�
furar dayake sha takamashi tuni yafara tari, joda tajuyo dasauri tabuga kara takoma cikin toilet, Mahmud yace sorry kanwata bansan kina ciki bane, a toilet take kyaro masa magana, yayana yaushe kadawo, Mahmud yace yanzun fa, anan nafara nayi missing din furar gwaggona, inama taje, joda tace tafita unguwa ne , uhm yaya zansa kayana fa, Mahmud yace oh so sorry kanwata bari ma zanje gun Ahmed

Yana fita tasauke ajiyar zuciya,  tafito takulle dakin ta Ida shirinta, akan dining yasame Ahmed Yana cin abinci, shima kuwa yarufa masa baya, Mahmud yace Ahmed dama kafada zamujo ne? Naga delicious haka, Ahmed yace a'a yanzun hafsa ta shirya mana su, Mahmud yace kai wannan hafsa tanaji da yayanta sosea,

Gaskiya duk wanda ya auri hafsa yagama komai arayuwanshi ga tsafta ga iya girki uwa uba ga ladabi da biyayya, abdallah yace bawani nan bazan baka itaba , Mahmud yajuyo yana kallansa yace to wayace maka santa nake , abdallah yace oho dae nadae gano inda kadosa, Mahmud yace kae nifa wlh bakomai believe me, abdallah yace to naji dae

Duk wannnan abun dasuke Ahmed baice musu uffan ba kawai abincinsa yake ci, har yagama yagoge hannunsa da tissue sannan yawuce room dinshi, Mahmud ma yagama yabisa, baisamesaba yasan cewa yana gurin wanka, sbd haka yahanye gado yana son yin bacci

Ahmed yafito sanye da jallabiya yace wannan iskancin fa, zakawani zo kahaye mun gado, bayan kasan ina fitowa bacci zanyi, Mahmud yabuga masa tsaki yatashi yashiga shima yayo wanka tareda alwala, sannan yabude wadrop yajanyo sabuwar jallabiya yasaka yatada sallah bayan yagama, yasakiran Ahmed, wanda har bacci yasoma dibanshi, Yace lfy malam kazo kana damuna bayan kasan natsani atadani ina bacci, Mahmud yace kayi sallah ne, Ahmed yace a'a banyiba kai nake jira , Mahmud yace kaifa Dan iska ne wlh, Ahmed yace idan iskancin kakeso sena koyamaka , Mahmud yagalla masa harara yadauki wayarshi yafita, se gidansu

Yana isa mom dinshi tafito tana oyoyo wazagani haka babu ko sanarwa, Mahmud yace mom nasameku lfy, tin dazu fa mukazo ina gidansu Ahmed acan nahuce gajiya, momy tace gidansu ubanka ko wannan Ahmed setayi tsamari nake ganinsa agidannan kaiko gakanan kullum yawon zuwa gidansu , Mahmud yace oh mom saunawa kikeson ingayamiki cewa shifa Ahmed haka rayuwanshi take se yayi sati agidansu ba'a San yadawo ba, rayuwanshi ce se addua,

Mom tace shikenan jeka huta, Mahmud yace yauwa my mom ina shukra da Khalifa, mom tace suna dakin abbanku, Mahmud yace suwai sai yaushe zasu girma kullum suna maqale daku kamar sababbin  haihuwa, mom tace ehh baruwanka kadawo zaka fara takurawa, yayana koh, Mahmud yatabe baki yashiga daga ciki,

Bayan magrib aka hadu falo domin dinner, abba yakalli Mahmud yace muhammad yaushe zaka fito da matane  nifa nagaji daganinka a haka, mom takarbe ahto nima dae wlh inason ganin jikokina tun inada karfina inmusu goyo , shukra tace lah bros kanada budurwa ne? Mahmud yagalla mata harara tuni tacigaba dacin abincinta, abba yace wai badakai muke magana bane, Mahmud yace toni abba mezance maka  banda wata yarinya danaga takwanta mun arai wlh, momy tace to idan bakada ita zamu nemomaka, Mahmud yace what? Niyarone ko kuma nidan dane dazaku nemamun mata, abba yace tokuwa idan bakaso kafidda mata kawai karshen zance, Mahmud yace bashine abunda yadace kuyiba addua zakumun allah yazabamun mafi alkairi agareni,

Joda tagama shirinta tsaf zataje skull takarbi kudin adaidaita gun gwaggo tafita kenan sukaci karo da abdallah yace wow c diz gul, so cute n veuryfull, joda tace ina kwana, dkyar ya masa dacewa lfy , yaushe kika fara skull haka kuma turkish intentional skull fah, joda tace ya Mahmud ne yasaka ni, abdallah yace Y? Joda tace kawai yanason ganin farincikinane, abdallah yace kamm Ai kuwa wlh dole nadauki mataki idan bahakaba zai karyatamun mafarkina, yarinyar Dana jima ina burin ganin girmanta , in cire sha'awarta dake dawainiya dani, joda taji shirun yayi yawa, tafice abunta

Yauma kamar kullum tafito tasame driver yanajiranta, banza tamasa sannan ta mike titi tana neman adaidaita, driver yakarasa gurinta yace hava madam wlh idan kikayi late nizakijawa hasara Dan allah kada kisa narasa aykina, joda tace kainifa bazan shiga motarkaba sae kagayamun, waye wannan ogan naka ahankali yace Mrs marafa ne, ido tazare Jin ance Mrs marafa tasan mutun dayane akecewa Mrs marafa

Cike da tsoro tashiga motar, tin ranar batasake yimasa musu ba duk yadda tayi sammako zata samesa yana jiranta haka kuma idan yakaita baya dawowa seya maidata gida, duk wannnan abun bata taba gayawa gwaggo ba aganinta bakomai bane , dama kuwa duk abunda ke faruwa na gidan dae2 dasau 1 bata taba gayawa gwaggo ba aganinta bakomai bane..........

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
     馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
        馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
           馃巹 馃巹 馃巹
              馃巹 馃巹
                 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 4鈨�0鈨�
Haka karatunta yacigaba da tafiya babu abunda ke takura mata , har tasaba da rashin hafsa, wata umma khalthum ce tinda tafara zuwa skull din takeson kawance da ita ganin irin hazakar joda,  joda tace lok kalthum kinganni nan nibakowa bace, banida kowa agarinnan se allah mu Fulanin daji ne dajin sokoto, mahaifina yarasu dalilin dayasa bana kawance dakowa, domin banaso indaukarwa rayutawa abunda yafi karfina

Khalthum tanisa shikenan joda dama dae bakison zama dakowa amma duk skull dinnan banga wanda yakaiki gata ba kodakuwa yafiki dukiya, dubi yanda malamai ke dar2 da bacin ranki , idan aka kawoki se antashi driver dinki yake komawa, breakfast sedai kizabi abunda kikeso abiya miki  , shin intanbiyeki akwai wani gata dayakae wannan ? Joda tace shikenan idan baki yarda daniba , amma kisani ni ba kowa bace face Yar aiki agidan, khalthum tace naji dukda dahaka, ni  I want be ur frnd, joda tace tom shikenan allah yabamu hakuri dajuna ameen, tin daga ranar suka zama wasu irin qawaye tamkar hanta dajini dukda basu taba ziyartar gidajensu ba, joda waya na burgeta amma bata iya magana

Yasir ya gabatarda iyayensa gurin dad domin shine ya wakilce iyayenta anyi maganar aure ansaka, sora 2mnth dazaran tayi   j . l . c , abdallah nacike da bakin cikin rasata amma yakudurci seya more ta kafun taje gamijinta, wata zuciyar tace taya hakan zae faru, okey Soyy zaka kulla da ita, to taya zan kulla Soyy da ita bayan tana tsorona, sekuma yace zan koyamata yadda zata soni da kyawawan halaye na nadaban kyautatawa tausayi kulawa etc, murmushi naga yayi na Jin dadi daga ranar yafara shirye2 yadda zae fara mata

Joda anshirya cikin bakin yadi mai flowers red tayi matukar kyau kamar ba joda ba , wannan yadin yana dae daga cikin kayan da Mr marafa  ke aykomata tin kan kayan make up cosmetic kayan sawa duk wani datake bukata sedai kawai taganshi, gashi bata ganin dad balantana tamasa godiya haka abun ketafiya, joda tawaye sosae fiye da zatonku

Tafito kenan zata tari taxi Sega driver dinta, dafe kanta tayi tace oh god, shi wannan driver sekace aljan bansan taya yake sanin schedule dina ba tsaki tabuga tashiga baya, basu tsaya ko inaba se gidansu khalthum, har ciki suka shiga, sannan tashiga parlour, wata mata nagani cikin shigar alfarma tareta da fara'a joda taxauna se kallon dakin take ruwa da lemu aka kawomata , sannan suka sake gaisawa, tace mama gurin khalthum nazo , mama tace ke kawarta ce koh ? Joda tace eh skull dinmu daya, mama tace ya sunanki, joda tace zainab muhammad, amma anfi kirana da joda,

Mama tace eyya aykuwa inajin zancen ki gun khalthum kullum batada zancen dayawuce na joda, joda tayi murmushi nan suka sha fira kasancewar khalthum bata nan, atake joda tashiga ran mama dazata dawo kuwa tamata shatara na arziki , haka takoma gida cike da murna dukda bata hadu da khalthum ba amma ranta fes domin kuwa mama akwai kirki

Tafito daga mota kenan sukayi kicibus da abdallah murmushi yasakarmta itama kuwa tamaida masa, abdallah yace kanwata daga ina haka, joda tace gidan kawata, abdallah yace shine baki kirani narage miki hanyaba kona rakaki, joda tajuyo cike da mamaki tace kae ne kake fadan haka? Abdallah yace balaifi na bane sako ne daga zuciyata, joda tace zuciyar ka fah?

Abdallah yace kwarai da gaske joda kinsan zuciya ta kan aykeka da sako a gurin da baka zato kuma ga wanda baka tsammani, joda tace lallai kam naga alama, dae2 nan takawo hanyar dakinsu tace ya abdallah sae anjima, abdallah yadaga mata gira c u ltr, ido da gangar jiki bazasu gaji da ganinki ba..........

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 4鈨�1鈨�
Joda tashiga dakinsu kanta duk yadaure gameda zantukan abdallah ita dae a iya saninta wanda ake so akeyiwa wadannan kalaman to amma koma yane zata jira yafurta sannan ta yanke hukunci, har tafara bacci taji muryar mai gadi yana fadan tafito ga yasir can yaxo , joda tace kainifa bazan iya tsayuwa ba kace yashigo , haka kuwa akayi yashigo dakin su gwaggo tabasu guri

Acikin firar sune sune yake ga yamata yagama gidansa kaf, gobe zasu kawo lefe, 3 week masu zuwa za'a daura aure, joda tasadda kai kasa tace allah yakaimu, haka suka sha firar su har zuwa wani lokaci sannan yamata sallama, tsalle tabuga sannan tashiga kwalawa gwaggo kira, gwaggo tace ke lfy wannan Kiran haka? Joda tace albishirinki gwaggo gobe za'a kawomun lefe, gwaggo tace wani lefe kuma bayan nace bana bukatar kowace bidi'a , joda tace ay yace dakanshi zaikawo, gwaggo tace to Allah yakaimu ameen

Ta shirya tsaf zataje skull tayiwa gwaggo sallama, kofar dakinsu ta hadu da abdallah, joda tace a'a ya abdallah ina kwana kaine anan, abdallah yasakarmta murmushi nine kanwata kintashi lfy, joda tace lfy lau, yasu hjy, abdallah yace qlw, yanxu se ina? Joda tace skull mana, abdallah yace ok toh Muje narakaki koh, joda tace dakabarshi , abdallah yace oh...nadae gano bakya San ganina atare dake, joda tace bahakaba ne, nagode kawai tacigaba da tafiya har gate sannan tashiga motar ta driver yajata suka wuce

Abdallah yayi murmushi  yace da sannu zaki shigo hannu yarinya, yajuya yashiga side dinsu, Jin ihun amina yasa shi tsaki yasan waccan antyn ce taxo, yana isa yagansu a parlour se hauka suke tsaye yayi akofa yana saurarensu, mansura na fadan magani yafara ci tinda Ahmed yafara daga wayana, tace anty kinsan me hadda tanbayana yake yagida, amina tace kai amma dae wannan malamin yayi wlh

Abdallah yabuga tsaki yashiga dakinsu ko gaisheta baiyiba, hjy tace ni wai narasa kan wannan yaron wlh, 2dyx dinnan yacanza hali, mansura tace yaji dashi can Dan iskan yaro kinaga ko gaidani baiyiba fah , hjy tace barsa zanji meke damunsa , mansura tace anty koh wlh har na hangoni kan jikin Ahmed, amina ta kyalkyale da dariya wlh kuwa anty zaki sha kamashi da laushi,hjy tace kai bansan iskanci maita zaki muna masa kiri2 koya, tin wuri kisake tunani kisauya ra'ayi kar kiyarda ya gane kina son yatabaki idan ma yatabaki kiyi masa bala'i kina jina koh, mansura tace inaji anty

Abdallah kuwa dakinshi yafada kan gado yarumgume filo duk juyi joda yake gani da murmushinta yana tuna dimple dinta, hakoranta fess ga wushirya atsakiyarsu, wanda takara mata kyau sosae da sosae runtse idonsa yayi yana hangosa manne da ita, lips dinta yariko yasaka anasa wani yarrr yaji ajiikinsa jikinsa narawa yakai nasa   baki kan lips dinta ahankali yake tsotsensu tamkar mai shan minti, yana kara lumshe ido can yaji anvude ganbu firgigit yabude idonsa uban tsaki yabuga ganin an katse masa tinaninsa, hjy ce tasamu gu tazauna, tace abdallah meyake damunka ne plss, abdallah yace plss mamma ki kyaleni plss, ganin haka yasa hjy fita dakin tareda cewa allah yahuci zuciyarka Dana

Tana fita yabuga tsaki yacigaba da juyi yana ganin kamar yana tareda joda,  gwaggo ta aika ma dad sako cewa za'a kawo lefen joda, dad yaji dadi yabada 30k yace a basu idan sunkawo , gwaggo tasha godiya kamar me, dasafe gwaggo tashiga kitchen tareda hasana mai ayki sukayi snacks da miya se meetpie, gwaggo tabada kudi aka siyo mata biyar malt ,exotic,hollondia, se 5 alive,  haka aka hada kayan abun sha'awa , karfe hudu narana Sega yasir da abokanshi su biyu, sunkawo lefe 1 set kaya tubarikallah dae2 buqata..........

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 4鈨�2鈨�
Shirye2 kawai akeyi gobe daurin auren joda da yasir kasancewar tayi junior weac , joda ansha kunshi da kitso dukda kitson fulani ne amma tasha kyau, dad yayi tsaye yagyara ma joda dakinta balaifi duk wannnan hidimar da ake hjy batada lbr abdallah kuwa kamar yayi hauka domin kuwa san joda yake kamar me , yayi kudi rin gayamata komai zaifaru yafaru , amma yagaji da dakon sonta

Joda takira khalthum da telephone tagayama mata, khalthum tayi matukar mamaki mezaisa amata aure daga yin j.l.c dinsu , cike da alhini tagayawa mamanta, haka suka dungumo suka zo tare, mama tayimata tirarika dayawa, da humra su kulacca da sauransu , koda suka isa gidan yafara jama'ar gwaggo da makota dayake bakowa yasan suba, khalthum kuwa fushi take da joda akan me zata boye mata har Seda akaxo final

Dakyar gwaggo tashawo kan khalthum tahakura suka ci gaba da hidimar biki , duk inda joda tasaka kafa khalthum na biye da ita, joda tace nikam wannan makalen name ne, khalthum tayi rau da ido hava joda ke bakya Jin kewar kowane, joda tace to ay bayau zanje ba yasir yace sena girma sosae, khalthum tace hmm wlh wanaki yake yau dinnan zakije gidan yasir kuma baxai sarara miki ba,

Joda tace kamarya kenan, khalthum tace a'a abun ma aurata mana, joda tace kenifa banganeba khalthum tace zokiji taje hannunta sukaje garden tashiga zayyane mata komai, joda kuwa tasamata kuka, khalthum tace ke dallah kimun shiru, dae2 nan abdallah yashigo dama kuwa yana kallon su ta window, yadauko kyalle yabata cak yatuna mata da Mahmud takarva ta goge hawayenta

Abdallah yace yace joda rana bata karya sedae uwar diya taji kunya,  ranar wanka ba'a boyon cibi, joda ina sanki ina sanki ina sanki 4rm d bottom of my heart, joda tace what? Ya abdallah kasan mekake fada haka, abdallah yaduqa kasa yace hava joda so baruwansa da nasaba kudi ko mulki wlh ina sonki so bana wasaba,

joda tace amma meyasa ka boye mun seyanzu dabamuda abun yi, abdallah yadago da sauri yace u mean kema kina sona kenan?Joda tashige cikin khalthum, tace ya abdallah ban isa ince bana sanka ba kaine mutum nafarko daya ji tausayina agidannan bayan hafsa, abdallah yayi murmushi yace nagode dakika fahimci haka kanwata

Atake taji tausayin sa naratsata , tace kayi hakuri ya abdallah kaddara tariga fata, koba komai nasan kafi karfina, abdallah yace nagayamiki so baruwansa da nasaba kudi ko mulki, joda tace hakane ina maka fatan alkairi allah ya zabamaka wata wadda tafini ameen, Jin sukayi hasana na kwalawa joda kira hakan yasa suka juya gabadansu, tace ya abdallah sae watarana nagode, abdallah yayi mata murmushi yadaga mata hannu, tuni hawaye suka ciko a idonta , khalthum dae sae binsu da ido take, wanka tayi tasake shiri abunta , sannan takoma takwanta, ahankali takira sunan khalthum, khalthum kinsan wani abu wlh tin safe nakejin faduwar gaba narasa dalili inata maimaita innalilahi, nakaranta qur'ani amma kuma se abunda yacigaba tsoro nakeji yana shigata se wani sanyi nakeji kamar zazzabi haka

Khalthum tadafa joda tace don't worry besty fargaba ce kurum kike yi insha Allah ba abunda zaifaru, kat agogon dakin yabuga dasauri tadaga kae tadubi agogon, khalthum tace kinkusa zama mallakin yasir nasan yanxu ana gama sallan jumu'a za'a daura auren , joda tayi murmushi tarungume filo tace khalthum kamar baxai yuba wlh mafarki nake khalthum kitada ni, khalthum tayi jugum tana kallan joda, can kuma seta tashi tadauko mata ruwa tabata tasha , tsam naga ta tashi taje tashiga dudduba wadrop dinsu dkyar taganta, wata jacket ce tadauko tasaka, tareda saka kanta aciki tana shakar turaren daya kusa shekara bai cire kamshi ba

2:30 dae2 kamar yadda aka tsara za'a daura auren joda da yasir akofar gidan Mrs marafa , dad shine wakilin joda se alh baushe shine wakilin yasir akan sadaki dubu 30, liman yafara gabatarda komai davada joda a mana kan yasir yasir , yace yakarba , dad yace dukda bani bane mahaifin wannan yarinyar ba, amma nabawa yasir gidana dake kan kasuwa, baushe yace bamu gane bakai bane mahaifinta, dad yace dama azatonku nine mahaifinta ay mahaifinta yarasu ayki suke agidana,

baushe yakalli yasir yace yasir dama kasan dahaka Yar ayki zaka aura, liman yace Dan allah kubari ashafa fatiha  mana, baushe yace shikenan allah yasanya alkairi har liman yafara bismillah se baushe yace dakata, Mrs marafa daga ina take, dad yace fulani ce Fulanin daji ne dajin sokoto, baushe yace what? fulani yo meya hadomu da fulani wlh Sam nafasa baxan bawa Dana izinin auren taba yasir yace hava baba miye aybun su? Baushe yace kai rufe mun baki babu aure tsakanin mahauta da fulani, Sam bazaka aure ta ba bada yawuna ba, haka yaja hannun danshi yana ta kuka suka bar gidan, duk yadda jama'a sukayi dashi Sam yaki yafahimta, dad yahasala matuka ga shi yagayyato abokanshi, dad yakira liman gefe zasu tattauna banjira Jin abunda zasu tattauna ba nagudu ganin irin facin ran da dadi yashiga gud uwa nayi se gurin su Ahmed

Ahmed yace Mahmud narasa meke damuna yau natashi da faduwar gaba , inaji kamar wani abu zai faru sedai bansan komeyi ba, Mahmud yace ka dauko al_qur'an mana ka karanta, Ahmed yace nifa inajin tsoro kuma sanyi nakeji sosae kamar zazzabi, Mahmud yace to Allah yakawo komai da sauki, nan Mahmud yafita shikuma yadauko jakarsa yabude yafidda wani dankwali na tsofaffi yadaura akansa, tareda wasu duwatsu kamar abun jigida yajimke sosae a hannunsa zuciyar shi na cigaba da bugawa......

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
    馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
        馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
           馃巹 馃巹 馃巹
             馃巹 馃巹
                馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 4鈨�3鈨�
Haka yawuni aranar cike da tsoro ga wani irin sanyi dayakejin na ratsa shi dakyar yasamu yayi bacci sannan komai yalafa masa, gurin joda ma haka abun yakasance bacci mai nauyi yakwasheta, acikin barcin ne taji hayaniya yayi yawa, tafarka hannunta rike da jacket tamanna ta akirjinta tafito waje Dan Jin meke faruwa, khalthum tagani zaune jugum, karasawa tayi kusanta tace lfy khalthum meke faruwa naga gwaggo tayi tagumi?  Khalthum tace joda duk abunda yafaru ga bawa mukaddari ne, duk abunda allah yahanama hakan shine alkhari agareka, joda tace  hakane wani abun ne aka rasa ?

Gwaggo ce tadafa joda tace zonan autana daki tashiga da ita taxaunar da ita kan cinyarta tace joda tin randa kuke haduwa da yasir bakitaba sanin Dan mahauci bane joda tace me? Mahauci kuma wlh bansaniba, gwaggo tace to mahaifinsa yahanashi aurenki saboda kinfi kowa sanin ba aure tsakanin mu da mahauta, joda tace iye yanxun yafasa kenan gwaggo ina son yasir fah, gwaggo tace hakuri zakiyi ba mijinki bane, joda tace gwaggo nikaina baxanso na aure mahauci ba yadda naga suna kiyayya damu,

Gwaggo tace yauwa yata naji dadi dakika fahimceni, joda tace yanxu gwaggo zai karbe lefensa koh? Gwaggo tace yace ya yafe amma ba abunda zamuyi dasu zansa a maida masa kayansa, joda takoma kan cinyar gwaggo tana ta murmushi wanda nakasa gane kona menene

Joda takankame gwaggo tanacewa gwaggo kirufeni sanyi nakeji, gwaggo tace sanyin lfy joda awannan yanayin na zafi joda tace gwaggo kisaka mun jacket dinnan gwaggo tadauko tasaka mata, tarufa mata bargo sannan tafita, joda tacigaba dafadin, sanyi2 inajin kamshinsa nazuwa, sannnnnnnnyiiiii ahaka har bacci ya kwasheta, Ahmed kuwa haka yawuni rike da wannan dankwalin tareda wani stone nikam narasa kona miye ne,

Dad yasa Kiran gwaggo yanabata baki akan abunda yafaru yace kiyi hakuri komai mukaddari ne watakila hakan shine alkhari, gwaggo tace kadena bani hakuri alh kai yakamata nabawa hakuri saboda ankunyata agaban jama'a, dad yace bakomai hakan shine dae2 allah yamusanya mata da mafi alkairi ameen, dad yace yanxun tacigaba da zuwa skull har muga abunda allah zaiyi zuwa gaba, anawa ra'ayin kibarta tayi sc skull sa'annan kimata aure, gwaggo tace bakomai indae hakan bazai janyo wani batanci agaretaba, dad yace bakomai insha Allah zan saka ido akan tarviyanta tamkar yayana, gwaggo takara rusinawa tana godiya, dad yace ay yiwa kaine wannan sedai fatan dacewa

Kusan sati guda joda nafama da kanta kwata2 takasa gane wannan yanayin, dkyar gwaggo tasamu taciyo kanta takoma skull bayan exam dinsu tafito murna ba'a magana domin tafito da 5 credit 3 A etc, malaman sun buqaci abata ss2 amma David yaki amuncewa yace oganshi yace abari tayi karatu mai kyau, dama joda bawani dadi tajiba domin bataso arabata da khalthum,  haka rayuwar ketafiya ba laifi komai datake buqata tana samu, duk inda zataje, driver dinta shiyake kaita

Joda tace khalthum yakike gani wai nayarda nakarbi Soyy abdallah kar nafada tarkon so daga baya kuma nazo nasha wahala domin wlh hjyrshi batada kirki ko kadan, khalthum tace kada kiduba wannan so baruwansa da wadannan ababen kedai kawai idan kina sonshi to fine, joda tace wa ni na isa ince bana sonshi handsome nefa, khalthum tace hmm joda kenan wlh kinyi saurin fara Soyy da wuri haka nifa nan dakika ganni senagama skulk kozanfara sauraren samari

Joda tace kekike ce ay badaya muke ba, ni nasan dakyar ne gwaggo zata bari inyi karatu, kinga kuwa gara nakula saurayi musa danta tin wuri khalthum tace gsky idan kikayi aure kin cuci kanki awannan tym din sc skull bakomai bane, kije kiyi karatu sosae kigan yadda jama'a zasu rika girmamaki, bama shegen dazai kara cewa wai ke Yar aiki ce wlh sedai a rufe zancen , joda tace allah koh? .............

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 4鈨�4鈨�
Joda tace lallae kuwa zan same gwaggo wlh natsani abunda akecemun wae Yar aiki sekace wata barauniya 馃槄 , khalthum tace tosae me Dan ance miki Yar aiki, ay ba shegiya aka ceba, joda tace kam yo ingama Dan kutumar uban daxae cemun shegiya wlh bakinshi yayi tsami, khalthum tabare da dariya, kae joda akwaiki da fada wlh , joda tace ahhh.....ay gsky ne, mu za'a nunawa asali, mahaifina Dan asalin Dan binji ne, gwaggo kuwa wani zubin ma, balarabiya ce Dan Yar masina ce kusaga Sudan , fulani ne amma ruwa biyu

Khalthum tace lallae iyakar asali kenan, joda tace ke bawannan ba, nifa wlh phone kebani sha'awa, khalthum tace kae joda akwai ki da kiriniya kinganni nan inada phone yakae biyar wadda abbana kisayamin amma suna a kwati na, ajiye se nagama skull, joda tace kae amma bakiyi ba wlh , khalthum tace nadae ji tashi Muje Dan allah tym x over

Driver ya ajiyeta dae2 gate tahangi abdallah rungume da hannayensa , yana mata murmushi, joda ta karasa cike da nishadi, tace kaddai ni kake jira haka? Abdallah yace kwarai da gaske kenake jira since baki dawoba yakarashe zancen cikin sigar shagwaba, joda takallesa ta kyalkyale da dariya, tace kae abdallah abun yara kakeyi , abdallah yace ay idan ina agabanki ni yaro ne seyanda kikayi dani, joda tace kana fasamun kae fah, abdallah yayi dariya yace hava dae my queen

Haka suka jero har kofar dakinsu yarakata yace idan kinshirya ina jiranki a garden, joda tace ok 30 minutes, abdallah yace hava Dan allah har 30mnt, joda tace bayawafa yanxun zanfito, tashige abunta ta barshi gurin murmushi yayi a ransa yace tafara kamuwa fah, gaba kadan zan cimma burina , yasosa kansa yashige side dinsu, mansura yasama kan dining tana lunch, yatabe baki sannan yace anty barka dazuwa, mansura dason girma tace qlw son hw x 2yd? Abdallah yace cool, mansura tace gud, yanxun Muje zaka kaini kaduna

Abdallah yazaro ido what, kd at diz tym mudawo yaushe, mansura tace kai dallah bansan iskanci zuwan Dan wa za'a yi badan kaba , abdallah yace kamar ya Dan ni? Mansura tace wannan kuma ba dole kajiba kawai kaje ka shirya, abdallah yace anty wlh ba inda zanje karshen mgn kenan yana kae nan yayi downstairs yabar ta, cike da alhini

Mansura tasami hjy tagayama ta duk yadda sukayi da abdallah, hjy tace  kibarshi badai sahun kafarshi akesoba kije garden gefen tanki akwai kasa kidebo seki zuba akofar shigowarshi dakinshi , mansura tace wow dz x my 6 kae anty kin iya hadoshi wlh, hjy tace nifa akace ay basauki ingayamiki, ni wannan shegen sudawo ma, muga ya nashi yanayin zai kasance a kanki

Mansura tace ohh...anty wlh gavana har faduwa yakeyi idan natunasa, kunsan me tin randa mukayi waya aranar ko baisake daga wayata ba kuma yayi blocking dina a WhatsApp yaki accept request dina a fb yaki following dina a instagram, bbchat snapchat, wechart, soma , imo palmtchart, hjy tace kai ya isa haka duk wadannan chrts din takeson kinayi ?Mansura tace eh mana danma Kin katseni ay basu kadai bane akwai twitter....hjy tace ke barni haka Dan allah dama acan kike karar da kudinki gurin siyen data, mansura tace kai anty akwai dadi fah baki da wata damuwa idan kina chrt, hjy tace allah yataroki charting ko sallah baya barinki, mansura tace kae anty inayi fah, 

Hjy tace kina me yau sallah kodaya bakiyi ba, mansura tasosa kae to ay zanyi, hjy tace kedai kika sani duk lalacina sallah baya wuceni, mansura tace inayifa anty se zani kwanciya nakeyi, sena hada duka, hjy tace kyaji dashi allah baya san hakan gwanda kigyara tin wuri shi isa ma kika kasa samun Ahmed nasan baxai rasa Jin lbrnki agari ba, tin wuri kisake tunani, dole kizama kamila kiyi watsi da samarinki kikama sa shi kadai hakan zaisa yatsaya kulaki.............

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 4鈨�5鈨�
Tafiya suke ajere suna shan ice cream abun su kae kana ganinsu kasan suna cikin farin ciki, abdallah yadubi joda yace bae zanyi tafiya fah, joda tace me? Tabata fuska yaushe, abdallah yace gobe amma bazan dadeba sati daya ne, joda tace sati dayafa ni wlh baxan yarda ba ay sati daya tamkar shekara daya ne agureni, abdallah yace calm down mana nagaya miki baxan dade ba kuma zamu rika waya da telephone, joda tayi kadi da ice cream dinta tanata buga kafa ni wlh baruwana dakai

Abdallah yadafe kanshi, Yace oh gosh ni yaxanyi da wannan yarinyar ne, nifa kawai saboda tayi missing nawa yasa nakirkiri wannan tafiyar, ina dawowa zan gama aiki, murmushi yayi yawuce hanyar gate, anan ne yahadu da dad, Yace ji man abdallah yafito amotarshi yace ahhh....abdallah yanzun dae an shiryu an daena shaye2 koh ? Abdallah yadafe kae yana wani murmushi ehh dad andeana, dad yace to yayi kyau allah yakara shiryamun kae ameen

Abdallah aranshi yace hmm nadae na me. uhm ay badan allah nadae naba inasamun bukata ta gun joda zan koma ga halina yanxun ma a matse nake,  ina zuwa kd zancigaba da harkata  ( Allah ya shirya abdallah ) ameen, dad yace mene kake tunani haka? Abdallah yace no ntn dad, dad yace to shikenan jeka allah yamaka albarka ameen

Su Ahmed angama wannan mission din murna gun Mahmud ba'a magana kullum baida zancen dayawuce na joda, haka zasuyi tafada da Ahmed domin shikuma in da wadda yatsana a duniya baifi joda ba, acewarshi itace sandin mura yakamashi, shirinsu sukeyi bawasa tin safe suka hawo jirgi sea birnin tarayya, Ahmed yakalli Mahmud yace kayi waya zakazo gida kuwa? Mahmud yace a'a kaifa? Ahmed yace dsame, Mahmud yace to ya kenan, Ahmed yace kainifa banasan wannan bahon yagane yau muka dawo yatsaremu agidansa, Mahmud yace waye bahon lallae Ahmed wlh bakada kirki, ina laifin Dan yakula damu ay bamukaday keyin tafiyar ba amma mubiyu kadae yake ma hakan tink mana sone kokuma me?

Ahmed yace kae dallah shut up ina ruwana dawani kulawarshi, nafi bukatar nasauka agidanmu , Mahmud yatabe baki okey sekayi waya azo adaukeka, Ahmed yace kai dae zakayi wayar idan driver ka yaxo sekuyi dropping nawa, Mahmud yace wannan kuma karyanka sedai kowa yanemi nasa driver n, indan kawai kayi waya kace azo adaukeka shine kake Jin haushi , Ahmed yace kae ya isheka fa haka, wani soldier dake jinsu yaxo yace A marafa kazo nayi dropping dinka mana

Ahmed yace kae kuma waya tasaka aciki dallah malam bace mun dagani, Mahmud yabuga tsaki yace ahaka din zan yi drop dinka, Ai wlh sedai kowa tasa tafish shesa, Ahmed yace dayake kasan gidanmu ba motor shine zaka wani tada ji jiya banza kawae , Mahmud yace oho dae nidae bazan iyaba indae baxaka iya waya azo adaukeka ba sedae ka tabbata anan gurin, Ahmed yajuyo afusace yace wlh zamuyi kutumar uba anan gurin idan baka mun shiru ba Dan iskan kawai,  Mahmud yayi murmushi yafidda wayarshi yasaka kira

Joda tafito daga dakinsu kawai taji wani irin sanyi na ratsata, ta lumshe idonta tacigaba da tafiya, dama kuwa tafito ne kawae saboda tasha iska, Jin karar Bude gate yasa ta Bude idonta dasauri, wani murmushi tasaki wanda yasa dimple dinta lotsawa ta dunfari motar aguje, tsayawa tayi jiran abude , motar kusan minti biyar shiru ahankali ta yi knocking din ganbun motar tana baxaka fito bane , Jin shirun yayi yawa yasakata lekawa amma kuma ba'a gani, atake tashiga buga kafar ta ni wlh kabude mun motar kona fasa glass din

Huuuuuu........taji wani sanyin nakara ratsata sakamakon, bude kofar da akayi idonta arufe ahankali tabude tana fadan kae koh 馃様
Kammm waxata gani 馃槼  , harara kallon tsana tsangwama bawanda Ahmed bai bita dashi ba, idonta kafff kan nasa takasa saukewa fuskarta cike da tsoro, tsawa yadaka mata Dan ubanki kibani hanya kafin in yi ball dake , ko motsawa batayiba balantana insaka ran zata basa hanya, hakan yakara basa haushi gashi dama yadawo da takaicin Mahmud kafa yasa ya turata dakarfi, kara tasaki tareda rike hannunta tana wayyo gwaggo nah.............

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
     馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
        馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
            馃巹 馃巹 馃巹
               馃巹 馃巹
                  馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 4鈨�6鈨�
Seda taci kukunta mai isarta sannan ta kamo hannun ta , tanata hawaye har tashiga dakinsu tasamu gwaggo bata waje, taje kan katifa tanata kukanta, har tayi bacci bata farkaba se kusan 3:30 zata mike tsaye ne se taji hannun yamata nauyi koda taduba yajuya gaba ya koma baya, jikin ta yahau bari wani zafi takeji har cikin zuciyarta , kuka yadawo sabo, azatonta zata iya daga hannun tafita aykuwa tana tabawa tabuga wata shegiyar kara duk wanda kegidan Seda yaji, gwaggo tafito da sauri tana fadan lfy , joda tafashe da kuka wayyo gwaggo hannuna zai cire gwaggo taxo tana dubawa tafara salati itama din rudewa tayi,

Tace joda meyasameki haka dakyar ta iya furta faduwa nayi ,gwaggo tace subhanallah Ai karyewa kikayi amma yanxu ay nabaki kina baccinki, joda tace tin dazu ne, nazata bkomai bane shine nazo nayi kwanciya ta, gwaggo tace yau na shiga 3 yanxu hannun yayi tsami sekinji azaba wlh, joda takara fashewa da kuka

Kansancewar dad yace duk abunda ake bukaqata anemesa, shi isa gwaggo takira hasana mai ayki tagayamata itama arude tashiga babban falon gidan tadanna bell, Ahmed dake saukowa downstairs yace ke lfy kike nemanmu, arude tace ranka yadade joda ce.....ya isa banason Jin wani bayani, hasana tace ranka yadade karyewa tayi ahannu kuma wlh hannun yabaude sosea, Ahmed yace what!?馃槼 karyewa garin ya, hasana tace faduwa tayi daxu shine tayi baccinta yanxun tafarka ne hannun har yayi kunburi, Ahmed yasaka hannu a aljihunsa yazaro bandir din yan dari biyar yabata yace gashi ku kaita clinic hasana tarisina tanata godiya

Karo nafarko da Ahmed yasaurari zancen daya danganci joda, dakinshi yakoma yacigaba da harkokinsa, kamar bashi ne sila ba, hasana nazuwa tabawa gwaggo kudin tareda mata bayani, gwaggo tace bara nadubo katinta na asibity, hasana da gwaggo suka kamata akafito da ita, Sega driver dinta yazo basuyi wata2 ba suka shiga se clinic dinda sukaje kwananan baya , suna fidda ita Sega nurses sunxo dakujera aka axata, sewani room asama, 

Su gwaggo suka rufa masu baya, gurin wani doctor aka kaita, suna ajeta zasu juya yace duka su tsaya dole se anriketa, joda kuwa tagalabaita se nishi take, hannun kadai yariko amma Seda tasaki wata qara, tuni gwaggo tafashe da kuka hasana tajata suka fita waje , doct din yace abasa allurar bacci kusan ukku ana mata amma taqi bacci se nishin wahala take dole suka kama aka riketa sosae bismillah yafara sanan yajanyo hannun yajuya shi dasauri yakoma qattt kakeji tuni joda tasume hakan yabasu damar daure hannun da kyau

Dayan nurse din tace sir amma yakamata abasu gado saboda taji jiki sosae kar sukoma gida alalata daurin, doct yace ehh ay se anwarware daurin duka zasu koma, anan suka fita suka barshi da ita, fuskanta yashafa yace allah yabaki lfy kanwata, bansan wani irin so nake yiwa yarinyar nan ba, tin randa nafara ganinta amma zanyi kokari in koya mata sona, indae har zata cigaba da zuwa nan asibitin,

Zan samu information akanta naji koyar waye miye asalinta, cikin wannan tinanin ne yaci tafara motsi, dasauri yataso yace sannu kanwata daga masa kae tayi, idonta duk sunyi jajir sun kunbura, tea ya hadama ta mai kauri yabata, takauce fuskarta, Yace hava kanwata ki sha mana, Jin yakirata da kan warshi yasa tadubesa sedai bata ganin fuskarsa tinda yasaka face mark ,

abaki yadinga bata har ta qoshi sannan yabata ruwa, zae fita ne tace likita sallah zanyi, cak yatsaya yajuyo yace kanwata sedai kiyi sallah aranki amma kinga bakya iya tashi alwala ma baxaki iyaba, joda tace toni ina gwaggo na, likita yace bari akira miki su yanxun idan su kike buqatar gani.............

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 4鈨�7鈨�
Nurse yakira yamata bayanin komai sannan yakoma office dinshi , akasa tasame gwaggo tamusu bayanin komai gwaggo tace nidae wlh zaman asibity badadi, hasana tace hakuri zamuyi za'afi kula da ita anan sabanin can ,gwaggo tace hakane yanxun tinda ga driver ke kije gurinta ni saena je nadauko mana abubuwan buqata, hasana tace hakane kiyi sauri ,gwaggo tashiga mota hasana kuwa tayi sama gurin joda,

kwance tasameta idonta arufe ahankali ta janyo kujera taxauna Dan atunaninta bacci joda keyi  , segata tabude ido , dasauri takarasa gunta tace sannu joda, joda tace yauwa
Bayan kamar minti shabiyar Sega gwaggo tadawo, harda abunci, joda naganin gwaggo tafashe da kuka,  hasana tace yo naji munafukar yarinya tindazu muna qlw Dan kinga uwarki zaki saka kuka, gwaggo tace kodai kin kwance tane , hasana tace cizonta dae nayi bare kwanta,

Ferfesun hanta da cabeg ne yaji sinadaran dandano se kamshi ke tashi, ga kuma sakwara da miya ogun, gwaggo tazuba aflate tabata, joda taki karba, gwaggo tace kae na manta hannun dama ne, amma wlh akwae aiki kafun ki warke , joda tace nifa banaci, gwaggo tace karyanki wolla dole kici, akayi2 amma joda taki ci, hasana tace bara akira likitanta, aikuwa segashi, hasana tace likita gata nan bata cin abunci , likita yanuna masu kofa alamar su fita, hasana taja hannun gwaggo suka fita , gwaggo tace shi kadai zaisa ta taci ayadda yake dinnan fuska ba annuri, kwananan baya ma shine muka samu yaduba ta kinga ko yanxu shine, amma fa likitan yasan aykin shi yana lallaba marasa lfy 

Kujera janyo daf da ita yasaka spoon acikin abuncin yafara bata abaki  , tanata yamutse fuska bai kulata ba, yacigaba da bata har abuncin yakare yazuba mata lemu da ruwa tasha sannan yakawo magani yabata, Yace ar u okey? Joda tace I think so, doctor yace menene? Joda tace bkomai ay bana Jin dae2 ne, doct yace taya kuwa xakiji dae2 bayan bakida lfy,

Yanxun gayamun taya kika fadi ahannu haka har kikayi muguwar karyewa? Joda tafashe da kuka, doct yace plss kanwata yihakuri bansan kuka zakiyiba ay da bazan tanbiyekiba , joda tace shine yaturani akan dakalin gidansu baya sona yatsaneni baya san ganina muryana ma bayaso, doct yace ya isa haka waye wannan damugunta haka ? Joda tace Dan mai gidan ne shine babba wanda nabaka lbr abaya, doct yace au ashe kingane nine nazata baxaki ganeba, joda tayi murmushi tace nagane ka magana, doct yace taya kika ganeni , joda tace wannan kamshin iri dayane Dana wancan tym din kuma kae dogone kamar wancan mugun, doct yace hava kidena hadani da mugu mana

Yanxun kibani labarinki, joda tace kamarya kenan ? Doct yace garinku asalinki skull dinki an others, joda kuwa tafara basa lbr kamar yadda tamasa ada, Yace anya wannan Ahmed din ba sonki yake ba, joda ta rufe bakinta Dan allah rufamun asiri kar yasake karyamun kafa, doct yace ina zaiganki ay duk wannan abubuwan take2 so ne, sonki yake bilhaqqi amma yakasa yarda da hakan inaji yanada feelings akanki sosea shine abunda kedamunsa,

Joda tace in possible wlh, ba yadda wannan yaron zai soni, yana Jin kanshi kamar wani sarki baya tsoron kowa ni wlh bana fata ko hanya tasake hadamu bare zuciya doct yayi murmushi shikenan naga kin tsorata a bar zancen kawai tinda baki so, amma meyasa kike tadi da abdallah, joda tace ay nagayama komai sona yake nima kuwa haka,

doct yarike baki yace ikon allah yanxun ke kinsan so, joda tasa hannunta tarufe  idonta , Yace dama kin bude ni baruwana, amma kiyi hankali da abdallah nasanshi farin sani ba shida kyau wlh, joda tace lfy lau yake nidae banga wani aybunshiba dayaga dae bata son zancen dole ya bari amma koba komai yaji relief akanta sakamakon Jin lbrnta da yayi...........

馃巹 FULANIN DAJI
N@ B aleeyu 馃挄 page 4鈨�8鈨�
Haka abun ketafiya kullum wannan doctor din shiyake kula da ita tinda sassafe zaizo yabata breakfast, haka lunch ma zaizo haka idan dare yayi shiyake bata har tafara sabawa  , Mahmud nazuwa kullum dubata tareda yan tsarabarshi, se  sun sha fira sannan yakoma, joda tafara Jin sauqi,

khalthum kuwa kullum tana hanyar asibity duba joda, ta tsinewa Ahmed yafi aqirga, joda tace kenifa na barshi da allah kifita harkanshi kawai, khalthum tace wlh joda da ace nice ke to wlh kuwa kodan uban waye bai isaba yatakani shi har ya isa ba soja ba bura'uba, joda ta rufe mata baki kae khalthum kiyi hakuri Dan allah kiyi shiru banasan irin wannnan zage2

Doctor ya ajiye biro dinsa yabi khalthum da ido to itakuma wannan wacece? Tambayar dayayiwa kansa kenan wadda ba'a amsa, yana saurarensu duk firar dasuke, sedai bai tanka ba amma yafahimci wannan khalthum din akwai zafi dukda joda ma nada nata zafin, shakuwa mai tsanani tashiga tsakaninsu da doctor dinta, sedai tana cike da kewar abdallah , ana haka Sega shi murna gun joda ba'a magana,

Seda tagama yimasa shagwaba sannan suka sha yabata hakuri kan dadewar da yayi, yana fita gwaggo tace joda wai ni miye tsakanin ki da wannan yaron ne? Joda tace bkomai gwaggo cewa yake ni kanwarshi ce gwaggo tace to wlh kiyi hankali dashi nidae wlh dama kin yanke wannan alakar atsakaninku, joda ta juye baki a ranta tace kuji gwaggo fah Dan baki san miye so bane shi isa kike cewa na rabu dashi

Gwaggo tace mekika ce? Joda tafara a'a in in dama cewa nayi, gwaggo tace dallah yimun shiru shasha yarinya ana nuna miki gsky kina kaucewa, joda tasadda kanta kasa tace Dan allah kiyi hakuri gwaggo, gwaggo tace bkomai ina kara jadda da miki bana San tarayyarki dashi karshen mgn kenan, joda tace gwaggo Dan  allah kibani lokaci yadda zan koyawa zuciyata rabuwa dashi bazan iya farat daya ba, wlh tausayin shi nakeji har kuka yake mun , gwaggo tace oh yaro man kaxa

Ahmed zaune kan gadonsa yana latse2 awayanshi, Mahmud yashigo yazauna, Ahmed yace daga ina haka, Mahmud yace daga gurin joda nake har tafara Jin sauki, doct din yasan aykin shi wlh, ni naso na ganshi na masa godiya, Ahmed yatabe baki yacigaba da aykinsa, Mahmud yace kozaka je ka dubata, Ahmed yagalla masa harara yace inje inyi uwarme acan? Mahmud yace uwarka xakayi acan da iskanci Dan kawai kaje dubata shine wani abun bayan koba komai akwai lada aciki

Ahmed yace ni kake zagin uwata akan wata banza , Mahmud yace yihakuri banji dadin zancen kabane shi isa, Ahmed yasadda kae yacije lebe yacigaba da aykinsa, wayarshi ce tadau ruri uban tsaki yabuga ganin wake masa waya , daga ganin yanayin shi Mahmud yagane ko waye kemasa waya, Mahmud yace da kayi hakuri dae kadaga wayar ka Mai sonka yafi makiyinka, Ahmed yace agareka hakan yake ni agurina gwara makiyi akan masoyi .......

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
    馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
       馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
          馃巹 馃巹 馃巹
             馃巹 馃巹
                馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 4鈨�8鈨�
Mansura nagani anci ado tamkar wata amarya se kwarkwasa take tana juya duwawuna, dakin Ahmed tanufa ba fargaba ko darr azuciyarta, knocking tayi nayi kusan minti biyar shiru ba'a bata izinin shigaba, hakan yabata damar murda key din dakin tareda sallama, Ahmed na zaune kan kujera yana kallo a system dinshi baida go ba , ya amsa sallamar tsaye tayi tana jiran dagowarshi, can da taga tsayin bamai karewa bane tace barka da hutuwa ranka yadade, banza yamata yacigaba da harkokinsa

Ahankali tasake cewa Ahmed ya hutuwa, nanma shirun ne yabiyo baya , mansura kam tadan tsargu , tasake cewa Ahmed mgn fah nake maka amma kamyimun shiru , Ahmed yadago afusace yace waeke mayyar ina ce,  mekikazo yi a dakina na nemiki ne kokuma ya? Mansura tajuya masa baya gudu kar yaga hawayenta, tace hava Ahmed kaso mai sonka koda kashi ne, bare mutun,

Ahmed yace ay kashin ma yafiki daraja agurina, da zanga kashin da kuwa zakiga yadda zan daukaka darajar shi sama da taki wawiyar banza jahila kawai get out yanuna mata kofa, bamu su mansura tafita amma me? Tana kae kofa tatsaya batareda tajuyo ba tace wlh Ahmed ina mai shaida maka cewa sena aure ka kota halin kaka, ka soni koka kini bashine damu wataba burina naganni a gidanka amatsayin mallakinka

Ahmed yace shege kafasa idan kika cigaba da cusa kanki a rayuwa ta to wlh zakiyi Dana sani na har a bada ,  mansura tace ok toh shikenan Muje zuwa nida kae, kasani bazan kara kawo kaina agareka ba, dakanka zakaje neman aurena, kasaka wannan a ranka!!! Ahmed yayi murmushin mugunta yace duka bokayen duniya da malamanku basu isa suja daniba,  ki koma kigayawa bokanku yayi kuskure da yayi tunanin zai iya galaba akaina, malaminki yaudaran ki yake ba abunda zai iya yimun, mansura tayi shiru Jin kalaman sa kana tafice daga dakin

Dakin hjy taje tafada kan gado, hjy na sallah ta Idar tace lfy mansura kika fada kan gado dakarfi haka ? Mansura tace inafa lfy anty kinji yadda Ahmed yace, nan ta zayyane mata yadda sukayi dashi, hjy tace indan wann karma ranki yasosu ina baki tabbacin Ahmed naki ne har kin samesa, mansura tace allah ko antyna, hjy tace sosea ma dubi nan, wani Dan karamun kwalba ne da turare aciki, hjy tace yana Jin kamshin wann shikenan angama dashi

Mansura tadaka tsalle wayyo dadi kasheni , hjy tace ungo kiyi hankali dashi dashi bakaramun kudi nazuba aka bani shiba har Niger aka karbo mun shi, mansura tace to ya ake amfani dashi? Hjy tace ajikinki zaki sakashi kisamesa, seki gayamasa cewa yaushe zae turo ayi mgn, mansura tace kae anty wlh ina Jin tsoro kinga yadda ya wulakanta ni yau

Hjy tace hakuri zakiyi tinda kekike nema ba'a gaggawa, idan kika bi komai ahankali zamuyi nasara, mansura tace to yanxu yaushe zan saka hjy tace bayanzuba se bayan kwana biyu, ni bani turaren kar kije garin rawar kan tsiya kifashe shi , mansura tace wae anty ina amina tin danazo bangantaba yanxu har 10:30 ace bata dawo ba, hjy tace ay wlh bataji ne nayi2 ta dena yin dare se ayita zagina agari bataji ne yanxun idan Ahmed zai fara yiwa mutane iskanci....shiru tayi Jin ihun amina gabadansu suka fito aguje

Ahmed suka tarar yana dukanta yana ball da ita hjy tasaka salati na shiga uku Ahmed kashe ta zakayi, Seda yamata lis sannan yace Al qur'an idan nakara ganin ki kinfita da irin wann shigar ta yayan arna wlh sena kakkaryaki bare kuma har kiyi dare haka tukun na ma gidan ubanwa kika fito?

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 5鈨�0鈨�
Cikin muryar kuka tace gurin bithday din saurayina Ahmed yakara hankata saurayi koh, to wlh kishiga taitayinki idan nakara ganinki kinfita koda get ne batareda izinina ba wlh se jikin ki yagaya miki
Kuma kisani kitattara kayan ki ki koma islamiyya on Sunday, hjy tace kae ya isa haka sekace wani ubanta zaka wani gindaya mata sharudda haka, Ahmed yace inada ikon yin hakan ne kuma babu ubanda ya isa yajanye wann tsarin, hjy tace koda uwarta ne, Ahmed yajuyo afusace yace koda ubanta ne!

Dae2 nan abba yashigo yace tabbas ko ubanta bai isa yajanye wann dokar ba bare kuma uwarta, hjy tabuga tsaki taja amina sukayi sama Ahmed yamaida kallansa ga abba yace abba barka dazuwa, abba ya amsa da lfy lau Ahmed yagajiya, Ahmed yace ba gajiya, abba yace Ahmed kayimun dae2 kacigaba da hukunta kannenka wann shi zai tabbatar mana dacewa koda mun mutu mun bar baya muna da wanda zai tarbiyan tarda yayanmu, Ahmed baice ,komai va yashiga maida belt dinshi daya Zare

Joda kam jiki Alhamdulillah tafara warwarewa, har wata kiba naga tayi yan kasusuwan jikinta duk sun bace, tayi cif cif da ita, yau satinsu biyu kenan, idan anyi lesson a skull khalthum tana tashi seta biya gurin joda tamata bayani sannan ta wuce gida, abdallah kuwa kullum yana kan hanya shida Mahmud narasa wayafi bata kulawa acikin mutun uku doctor ko abdallah kokuma Mahmud dukda khalthum ma ba'a barta abaya ba

Abdallah yakalli joda yace bae yaushe zaki koma gida? Joda tace nima bansaniba ask doct, abdallah yace okey ana haka Sega doct ya shigo, abdallah yabasa hannu suka gaisa, Yace doct yaushe za'a bata sallama ne, doct yace itace tace maka tana bukatar sallama? Abdallah yace no, doct yace gud taji sauqi ne har tana iya komai sa hannun koh? Abdallah yace no hava gashi kana gani , doct yace to me kake bukata da abata sallama tinda ba kula zakuyi da ita agidaba kamar yadda yakamata

Abdallah yace shikenan allah yabaki lfy kanwata ameen , joda tace doct mura kakeyi ne, doct yadaga mata kae yacigaba da rubuce2 joda ta tabe baki bansan meyasa yake bata ranshi ba idan yaga abdallah agurina , sedai kayi ni bamai rabani dashi shine hasken idaniyata abdallah yace bae zanwuce sekuma night, joda tace tom amma Dan allah karkayi dare sosea kamar yanda kakeyi, abdallah yace kinsan fah inada abubuwa agaba nane matse wa nake ina lekowa gurinki,

joda tace nadae gayama idan nayi bacci karka kuskura katadani, abdallah yayi murmushi to ranki yadade , yana fita doct yarufo kofar dakarfi har Seda joda ta tsorata, tace lfy doct? Ba lfy ba shine amsar daya bat! Joda 馃槼 meyafaru? Kace mura kake kuma gashi muryanka ayanxu qlw, doc yace yess , ba lfy ba, banason ganinki da wann yaron zai bata miki tarbiya yaron dake shaye2 , joda tace ya isa haka bakada wann hurumin na shiga tsakanina dashi koma dae meyake sha ina sonsa ahaka kuma babu wanda ya isa ya rabani dashi , doct yadaka mata tsawa dacewa how dare you ni zaki gayawa mgn tuni joda tashiga taitayinta

Doct yace b carefull you do not know me , joda ta kankame jiki tafara kuka abunda yatsana kenan kukunta glass dinshi yasaka yabar mata dakin , yana fita tafara tunanin anya kuwa ta kyauta hakan datayi, yinin ranar baidawo ba baixo bata lunch ba bare na  dare haka tawuni da yunwa  , damuwa fal aranta duk wanda yaxo dubata haka zai hakura yakoma anrasa kanta ,Mahmud da abdallah atare suka zo tana Jin shigowarsu ta lafe kamar mai Jin bacci...........

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 5鈨�1鈨�
Ahmed yafito daga room dinshi zai shiga kitchen yahada coffee , mansura  kuwa dama tana labe kawai segata aguje dae2 nan Ahmed yafito suka hadu da juna dasauri Ahmed yaja dabaya yana kokarin rufe hancinsa 馃檴 Jin wani kamshi tareda wani yanayi yana shiganshi, ganin haka yasa mansura yin sauri takarasa kusansa ta ware hannayensa Ahmed yashiga juye2 da kanshi yarasa inda yake masa,  dadi kasa yadinga yi har yakai kan carpet yazauna

Mansura tace yade Ahmed, ahankali yadago idonsa dasuka kada sukayi jajir yace bakomai ina son na kwanta, mansura tajanyo hannunsa sukayi room dinshi, kan gado ta ajiye shi , ido kawai yake binta dashi, mansura tace mekake bukata ne, Ahmed yace bacci nakeson yi , mansura tace bismillah , kwantawa yayi tareda wasu tinanin wadanda yakasa gane kansu, mansura tadaka tsalle tayi dakin hjy da gudu tafada kanta I love you my cwet anty wlh yakamu, anty kinga kuwa  yanda yake kallona, hjy tace dakyau seki fara aykinki bawasa

Karfe 2 dae2 Ahmed yafarka tareda rike kanshi dayakejin yana juyawa , yana son tuna abunda yafaru amma yakasa , wanka yayi yashirya cikin kananan kaya , yana kokarin fita wayarshi tadau ruri, new number ce saboda haka baidaga ba Seda tayi kusan 3 miss call sannan yadaga tareda fadan yess, Jin muryar mansura yasa shi Jan tsaki tareda fadan ya ake ciki? Mansura tace inaso karakani shopping ne, Ahmed yace kinga na miki kama da mai rakiyar mace

Mansura tace shikenan tinda baka sona, Ahmed no kigane banda gud tym ne amma zan baki driver, mansura tace ni idan baxaka kai niba kabarshi kawai kafi driver agurina, Ahmed calm down mana zaki iya barin firar har zuwa night yanxun inada abun yi ne, mansura tace allah yakaimu, my man I love you.....Ahmed yace uhm.....Thanks mansura tace au baxaka cemun you love me ba, Ahmed yace ay base nafada ba fadanshi bashi yake tabbatar dashiba, mansura tace dukda haka nidae nidae inason Jin wann kalma daga bakinka , Ahmed yace sena dawo I'm busy ya tsinke wayar yafita

Mansura tace ay day tinda baxaka iya cewa baka sona ba komai yayi nakusa kammalawa da matsalar ka, Ahmed kuwa yana Jan mota yana mamakin kanshi shi kam yarasa meke damunsa akan mansura yana Jin wani feeling akanta yarasa ko miye , yafe yake yana shan wakar ice prince. Waya yake da hafsa cike da kulawa yanata tambayar yakaratu ba abunda kike bukata hafsa tace bakomai bruhh , sedai ina neman wata alfarma guda daya Ahmed yace yes go on " hafsa tace bruhh plss ina son mgn da joda, Ahmed yace hafsa zaki fara koh? hafsa tace sowie bruhh, Ahmed yace dont lemme warn u again , hafsa tace bruhh.....shhhh yafada bana San Jin komai dole tayi shiru tareda Jin wayar ma ta tsaneta duka

Joda kwance abun duniya duk ya isheta tin ranar bata kara saka doct a idonta ba sedai yaturo wata likita tadubata idan joda ta tadubata ya doct baya xua se tace mata yana busy ne, gashi ankusa bata sallama tinda hannun yayi kyau yanxu tafara motsa shi da kanta yau sunada text skull saboda haka tin wuri tashirya driver yaxo yakaita a skull se xua dubata ake ana mata sannu karfe 12 dae2 suka fito exam principal yatava izinin komawa gida ganin yanda take

Dama kuwa driver na jiranta tana fitowa suka sa kae se asibity dae2 kofar shiga asibity tahadu da Ahmed Yana fitowa dumm taji gabanta yafadi dasauri take ja dabaya baya, Ahmed kuwa yatsuramata ido yana kallan shigarta acikin uniform, ido yazare 馃槼 naga ya yada key din motar shi ya na fadan jodaaaaaa鉂� wani rin tsalle naga yayi yacab kota suka fada gefen titi ,  mai motar yafito da niyyar basu hakuri sekuma yayi turus ganin irin kallon da Ahmed kebin joda dashi ita kuma idonta arufe..........

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
     馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
        馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
           馃巹 馃巹 馃巹
              馃巹 馃巹
                 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 5鈨�2鈨�
Joda ta turasa da karfi da koma gefe tana maida nunfashi , Ahmed yamaida kallansa ga mai motar yace kae mahaukacin inane kana ganin ta tana yowa baya da baya baka iya yi mata horn ne? Mutumin yace to ay laifin ta ita batasan kan hanya take ba , Ahmed yace bazaka gane laifin ta bane Seda ace ka maketa wlh daka san katakarowa kanka bala'i,

mai motar yace yi hakuri ranka yadade, amma dae kanason matar nan taka dayawa,  Ahmed yace what? 馃槨 ubanwa yagaya maka cewa matata ce, Mutumin yace am sorry irin yadda ka tsorata  ne da kuma yanda naga kana kallanta yayi kama da yanayin so mai babban Al amari aciki , Ahmed yace bansan raini kagan namaka kama da banza ye ne, wann kanwata ce yanuna ta batareda yakalletaba Mutumin yace ayya gsky kana son kanwar nan taka dayawa, shi isa kuke matukar kama big eyes dinnan naku iri daya da sexy lips dinn , Ahmed yadaka masa tsawa, tuni yashiga motar shi yabar wajen ganin yanayin Ahmed

Tin randa Ahmed yafurta cewa kanwarshi ce takasa daena kallanshi se mamaki take yau itace Ahmed ya kecewa kanwarshi ce, murmushi naga tayi wann shine nabiyu ko menene oho" Ahmed yadauko jakarshi ko kallan inda take baiyiba yanufi motar shi  Kamar ance yajuyo, yagan tabishi da ido wata harara yaballa mata tuni tajuya da sauri, ashe akwae ruwa agurin jinta kakeyi tisss tafada aciki kuka tafashe dashi wayyo gwaggo hannuna wayyo hannuna Ahmed yayi Jim kadan sann yafito yaganta se hawaye take, tsaki yabuga yace zakumin shiru kosaena kara karye miki hannun

Joda ta dukadda kanta se sheshsheka take wayarshi yaciro yakira wata nurse cikin kankanin lokaci Sega su su uku yace ku kaita sama a dubata yana kai nan yafice yayi gurin motar shi " joda kam se kuka take har suka isa da ita sama, cikin muryar kuka tace Dan allah kukiramun likita nah, dayan nurse tace karki damu yanxun zaizo zanmasa waya, joda tacigaba da kuka  sunata bata hakuri, kwance daurin sukayi sann suka duba, dayar tace anisa dubamun ay kamar taji sauki,

Wani doct ya izo mata yace bashida lokacin zua, shi yaduba daurin yace base ansake wani ba taji sauki sedai kawai Dan wann faduwar datayi ne amma zua 5dyz za'a bata sallama, joda taji dadin Jin hakan Dan kuwa ta qagu da zaman asibityn, baccinta tayi na kusan awoyi biyu se kusan la'asar tafarka sann taje tayi kowace sallah takoma kwance tana tunanin irin yadda doct yadau abu dazafi haka,  abunci aka zuba mata amma bawani cin kirki tayi masa ba sama2 taci takoma kan gado

Abdallah yashigo rike da Yar ledarshi, yanata fa man yiwa joda murmushi joda kuwa ta kawadda kanta gefe, Yace kanwata nayi laifi ne? Joda tace a'a kawai banajin dadi ne, abdallah yace meyake damunki, joda tace bakomai kawai dae bana Jin dae2 ne, abdallah yace ayya bae konakira doct ne adubaki, joda tace a'a bana bukatar hakan bacci zanyi, dayaga dae dole bata san firar ya ajiyemata ice cream dinta yayi mata saeda safe

Mansura tareda amina suna saukowa downstairs, dae2 nan dad yafito room dinshi aikuwa yayi kamar baigansuba, amina tace dad barka da fitowa yaamsa da yauwa, mansura ma tagaidashi yakarba bayabo ba fallasa, mansura tace jeki kiramin Ahmed amina tace what? Ahmed fah sokike ya bibbigeni a banza wlh baxan jeba yaushe ma kikayi wann matsayin keda ko Kin samesa a dakinsa wulakanta ki yake bare kuma ya amsa kiranki ay seki saka ya sanbadeni wlh yanxun zaifito ya shuka miki rashin kunya

Mansura tace dakata kiga, wayar ta taciro tasaka kira Seda tayi ring yakai biyar sann yadaga, amina tace ahto, dama dae kin hakura da wann miskilin dayafi, mansura tace hava babyna yabaka daukan waya, Ahmed yabuga Dan tsaki sann yace ina toilet ne, mansura tace ok kasameni a dining akwai maganar da zamuyi, Ahmed yace bacci nakeji sedai kayi bari har natashi gobe kenan understand? Mansura tace hava kae wae goma mutun yake da bukatar ganawa dakae seka kawo masa naka uzurin na daban idan baxaka zo yanxuba abar zancen kawai............

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 5鈨�3鈨�
Ahmed yadaga kafada yace alright , amina tabushe da dariya tace mena ga yamiki anty wlh ko dad baya masa wann ikon kince dole se yanxu, ay wann dolen dakika ce shizai ha nashi xuwa koda kuwa yayi niyyar xuwan, mansura tace ke wlh zanci ubanki kikama mun bakinki Yar iskar yarinya....shiru tayi Jin kamshin turaren sa nadosota , dukansu suka juya Dan ganin ko waye  amina ta Zare ido 馃槼 can a maqogaro tace bruhh,  binta yayi da harara tuni takama hanyar dakinsu

Mansura ta washe baki tace ashe zakazo durling amma Seda kabatamun rae, murmushi yamata wanda yafi komai ruda ta, kujera tajamasa yazauna sann tadauko lemu tazuba musu tareda cup, bismillah tace masa Ahmed yace thanks. menene maganar? gabanta yashiga faduwa tadaure dae tace Ahmed nasan kasan cewa babu wani namiji danakeso a duniya sama dakae akanka zan iya komai zan iya bada rayuwa ta akanka banajin......

 ya isa yadaga mata hannu, let go 2d strength point, mansura tanisa sann tace Ahmed inaso katura gidanmu neman aurena! What aure kuma? dama nace miki zan aure ki ne ? Mansura tace fyn yanxun katabbatar mun dacewa baka sona, Ahmed yace bahaka bane amma naga dae bawani dating muke dake ba kuma ni bantaba yimiki zancen aure ba hasali ma banida ra'ayin aure ayanxu, mansura tace lamme ask you menene ribar Soyy? Ahmed yace aure, mansura tace gud sbd haka aure zamuyi bafashi shine zaibada tabbacin muna san Juna,

Ahmed yabita da kallan mamaki kana yace umurni kike bani ko kuma shawara ? Mansura tace shawara dae  Ahmed yace gud to zanyi shawara da zuciyata, mansura tace hava Ahmed nida kae munasan juna tome nawani shawara, Ahmed yace ni bance ina sonki ba shawara kuma dole ce adukkan lamari, mansura tace kenan baka sona Ahmed yace waeke meyasa kincika mita ne hava yaja tsaki yayi dakinshi

Amina dake labe tace tirkashi kenan angama da bruhh amma wlh baga badae ba se yayi kamar zai warware komai sekuma yakasa, amma anty zakici ubanki wann ba namijin so bane, mansura tace mekike sakawa ne haka, firgigit tafarka daga dogon tunanin da take, , tace bakomai anty ina mamakin yadda bruhh ke yarda da bakon Al marin dake zuwar masa , mansura tace nan gaba sekinga yana driving dina, amina tace hehehe aykuwa da nabada gold dina sadaka

Ahmed yafada kan ga danshi se juyi yake meke damuna wann bakon Al amarin fah meyasa bana iya gaya mata bana santa , meyasa zanbiyewa umarninta allah kamun gata fadawa yayi kan gadonsa yana Jin haushin kansa meyasa ma ya amsa kiranta sekace wata u warshi, wayarshi yajanyo yakira Mahmud ring biyu yadaga hello mah kazo yanxun ina gida akwai matsala, Mahmud yace subhanallah ganinan zuwa momy zankai unguwa idan nasauketa zan biyu , okay  sann ya tsinke wayar

Har bacci yasoma dibanshi Sega Mahmud yashigo zaune yatashi, Mahmud yace gani mod ince dae ko lfy daga ninka nasan ba lfy ba meyake damunka, Ahmed yace wato Mahmud narasa abunda kedamuna wlh nakasa yimata gardama ina biyema umarninta Al hali basanta nakeba nakasa furta mata cewa bana santa bansan meyasa ba, Mahmud yace waye ita haka ? Ahmed yaja dogon nunfashi sann yace mansura kanwar hjyr gidann, Mahmud yayi murmushi yace why not ka aureta tinda tana sonka koba komai zaka moru domin mace idan tana sanka zata iya yimaka komai arayuwa sabanin hakan kuwa se hakuri

Ahmed yace kana ganin aurenta zai zamemun alkairi senake ganin kamar batada kyakkawar tarbiya Mahmud yace shedanne ke kawo maka wann aranka koya take auren irinsu jahadi ne babba yafi auren wadda kake da yakinin cewa tana da gud behaviours, Ahmed yace amma dae nasha gayama maka nafi ra'ayin mace karama wann kam ay kona girmeta kadanne, Mahmud yace karka duba wann ba'a kanka aka soma ba.............

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 5鈨�4鈨�
Ahmed dae abubuwa sun kwance masa , yana Jin tsoron yadda zai tinkari dad da wann zancen kae bama dad ne matsalar ba a'a abba ne keda tsaurin ra'ayi , bakinshi yatabe yace anyhow dae ni ita nakeson aure, dama kuwa aure suke son inyi saboda haka ba fashi aurenta kadaine kwanciyar hankali na, ayadda nakeji dinnan kamar ana mintsilana dole na aureta da wann tinanin bacci yayi a won gaba da shi, uhm....tirkashi masu karatu yakuke hango wann Al_amarin ?

Yau dae kam ansallami joda, amma bawani nishadi a fuskarta, dayan nurse tace hava joda ko bakya farin ciki da wann rana ne allah yanuna miki kin bar asibity nan lfy tareda sa'a, joda tace ina muryana sedai kawai damuwana daya ne ina son likitana domin in mishi godiya, dayar ta kalli daya sann tace keday kiyiwa allah godiya kawai , amma wann likitan dakike ganin bahagon namiji ne ba'a iya yimasa dae2

Gwaggo tashigo tace wae mekike jira ne tindazu driver yake jiranmu awaje haka dae tafito asibity bada san ranta ba, jikin ta bakwari , driver yagida ta asma dae wani iri,  suna isa gida tabude ganbu tafita bata jira gwaggo ba, amma me takasa gane kofar dakinsu yadda taga angyara shi dole ta tsaya jiran gwaggo taxo gwaggo taja hannun ta tace zonan joda , suka shiga ciki joda kam se bin gurin da kallo take

Yadda taga ansaka musu  furniture, da set din kujeru masu kyau ga kayan kallo da fridge, komai dae angyara gakuma akwatinta biyu cike da kayan sawa tin kan jallabiya atanfa shadda less material, ga cosmetic nan, atake taji damuwarta ta yaye Gwaggo wayamana wann hidimar haka, gwaggo tace bawan allah yawuce mai gidann ne nidae gani nayi kawai ana shigowa da kaya ance za'a gyara nazata ma korarmu akayi ashe azziki ne ke bibiyarmu joda tace allah yasaka musu da mafificin al_khairi ameen

Wanka tayi tadakko daya daga cikin kayan da aka kawo mata tasaka doguwar riga ce red har kasa takamata sosae simple make up tayi taje gun gwaggo tace Dan allah gwaggo kirabamun gashinan nawa biyu ya isheni wlh, gwaggo ta taje mata kan sann aka mata kitso gida biyu haka tazubo abunta agaba kamar wata babyn india, haka kawai taji tana sha'awar fita waje, dayake weekend ne ba skull kuma ana hutu islamiyya,

Dae2 swimming pool tazauna tasaka kafafunta acikin ruwan tana wasa dasu, wani iska yakada tareda sanyi da kamshi hannunta tasaka ta kankame jiki sosae tareda lumshe idonta, Jin takon mutum na zuwa yabata damar bude idonta, takasa tafara kallon mai xua murmushi tayi ganin kafafun Abdallah tace kaidae kullum cikin saka wando 3Q kake , tasaye ta tashi da niyyar kara masa wata magana abun data gani yasa ta shan jinin jikinta, dasauri tajuya baya tana komawa da baya baya

Wani shu"umin murmushi naga yayi wanda na tabbatar na mugunta ne, bata ankara ba taji yafada tussss acikin ruwa dae2 nan Ahmed yajuya baya zai tafiyanshi joda ta kwala mishi kira yayan hafsa......Dan allah kataimakamun ban iya fita ba, tana mgn tanayowa saman ruwa cak yatsaya batareda yajuyo ba sed yadade ahaka shi baitafi ba kuma shi bai dawo ba

Har tacire ran zan dawo sekuma taga yajuyo fuskar nan ba fara'a kamar baitaba dariya ba, Seda yakawo dae2 ruwan sann yaballa mata harara dasauri tadena kallanshi, hannu yamika mata tamasa banza takara kankame jikinta, Seda yadaka mata tsawa zaki zo kona tafiyata, cike da tsoron abunda zaimata, tabasa hannu yatashi tsaye yacabko ta dakarfi, Sega joda kan kirjin Ahmed 馃槣 dasauri yatureta yana mata wani mugun kallo yanunata da yatsa, sann yace Dan kince yayan hafsa yasaka na taimakeki, domin ni bayayanki bane, karma kiji ranan nace miki kanwata kizata ko dagaske ne taimakonki nayi kawai..........

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
   馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
      馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
         馃巹 馃巹 馃巹
            馃巹 馃巹
               馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 5鈨�5鈨�
Ahmed yajuya yabarta sororo, aranta kuwa tace koma dae menene badae ka fidda niba toh Alhmdllh , dakinsu taje tacire rigar tacanja wasu kayan tashanya rigar , zazzabi yasoma rufeta, ga mura atake tafara sneezing, telephone tajanyo tasaka Kiran likitanta cos yagaya mata cewa duk abunda yafaru shi zata nema, Seda wayar tagaji da ringing sann aka dauka wata nurse ce tace baya nan ay bakowane tym yake xua asibity ba, seyaga dama

Amma zan miki wata nasifa zan kira miki shi, mexa'a gaya masa, joda tace mura da zazzabi kedamuna ga ciyon kae , nurse din tace alright, zangaya masa allah yasama zai daga wayar, joda ta tsinke wayar takoma kwance, gwaggo tashigo tasameta cikin bargo, tace  lfy joda, joda tace gwaggo mura ne da zazzabi, gwaggo ta dafe kanta tace ohhh ni manga ke kam gakinan kullum ciyo kamar Yar kaza,

joda tace gwaggo ruwa fa nafada aciki, gwaggo tace toh garinya hakan tafaru? Joda tace tintibe nayi, gwaggo tayi tsaki ayke bakya rabuwa da tsautsayi sekace amarya , joda tayi murmushi tace nidae gwaggo fura in akwaita, gwaggo tace babu sedai in miki yanxu idan ita kike bukata tinda akwae garin tsaba, joda tace gwaggo bansaki wahala ba, gwaggo tace shin fura dae kikeso koh? Joda tace eh, gwaggo tace toh shikenan sedai xua magrib kam, joda tace toh gwaggona ngd

Gwaggo tashiga kitchen tareda hasana dayake duk aykin da gwaggo zatayi se hasana ta ta yata, ruwa aka fara dorowa atukunya  sann aka dama garin, suna fara boiling  aka zuba mulmulen garin kafun kace me har yadafu , hasana ce ta daka shi sann gwaggo takarba aka dama tareda nono, plastic aka cikawa dad aka saka masa a fridge , joda nasahan fura taji sallama kuma da alama namiji ne dasauri tasaka hijabi wanda tagani ya sata yin murmushi lah馃槉 doctor ashe zaka zo , Yace ba wann ba kan hanya nake allura zan miki ga magani sena wuce atake joda tafara 馃槴 ni wlh bazaka mun allura ba

Baki yasaki yana kallanta can kuma se tace kae wae koba a asibity ba seka saka face marks , kuma kullum da glass a fuska, doct yace eh haka nake, joda ta tabe baki shikenan dkyar tayarda yamata allura da kuka da komai Seda gwaggo tafara yimata fada sann tayi shiru magani ma dakyar tasha shidae baice mata komai ba sedai yayi murmushi

Yagama yayiwa gwaggo sallama, gwaggo tace nikam dann wayake biyanka ne ? Doct yace allah, gwaggo tace shikenan kuwa ka gama mgn, yana fita abdallah nashigowa, bae yade yau banganki ba joda tace kaedai wlh zazzabi da mura,  abdallah yace ayya baby na allah yabaki lfy ameen, bude bakinki nabaki chocolate, joda Jin ance chocolate da sauri tarufe  idonta

murmushi yayi yauwa babyna yasaka mata dae2 nan gwaggo tashigo mugun kallo tabi abdallah dashi sann ta kwalawa joda kira dasauri joda  tabude idonta , gwaggo ta bala'in daure fuska kana tabita da harara joda tashiga rawar ido jikinta yadauki bari ,gwaggo tarungume hannuwa tana musu mugun kallo , Abdallah yashiga soshe2 gwaggo ina wuni? Gwaggo tace da ban wuniba zaka ganni anan, meyakawoka dakinmu, kaxo ka koyawa yata lalaci koh? Abdallah yace a'a wlh inna kiyi hakuri ni sonta nake bakomai ba

Gwaggo tace dakyau idan sonta  kake nabaka sati daya katuro mun iyayenka, idan kuma rayuwarta zaka bata tokuwa zan hadaka da mahaifinka, joda tace gwaggo wace irin mgn ce wann abdallah baya nufina da komai wlh ko yatsana baitaba tabawa ba wann ma shine nafarko kuma shaukin so ne , gwaggo tawanke ta da mari, lallae na yadda so makaho ne, tinda har joda take kallon idona tace shaukin so.........

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 5鈨�6鈨�
Abdallah yace allah yahuci zuciyarki gwaggo yaraba ta gefen joda yawuce, gwaggo tarakashi da harara  , joda tafada kan katifa tana kuka, gwaggo tayi waje tabarta cike da haushi, abdallah kuwa naxua dakinshi yadauko win yasha yace lallae wann matar zata kwabsa mun baxata watsar mun da plan ba nan da sati dayan data ce zan cika mata ayki   , wani guntun murmushi yayi yacije lebe

Ahmed yashirya tsab yanufi dakin dad dinshi, zaune ya samesa yana karatun jarida , Ahmed yayi sallama dad yakarba tareda murmushi, Ahmed yace dad gud mrng, dad yace mrng hw ar u son, Ahmed yace am glad 4u dad, dad yace gud, Ahmed yakallesa yaga shi yake kallo , dad yace yess kae nakeji yau nasan akwai mgn daga ganin wann bakin naka , Ahmed yace eh dad dama wae zancen auren nan ne dakace , nasamu mata, dad yace wow I can't believe you fah, Ahmed yace serious dad ay bana wasa dakae

Dad yace gud 4u son a ina take kuma Yar waye, Ahmed yace kasanta dad, mansura ce, dad yace eye wakace kamar banji da kyau ba Ahmed yace itada din da kaji mansura, dad yace wace mansurar, Ahmed yace kanwar hjy ta nan gidan, dad yace what ar u in sense ? Mansura fah kace yarinyar da bata ganin idon ubanka da gashi bare kae wai tsayama tukun yaushe kuka fara dating da ita da har abun yakae ga aure , Ahmed yace oho dad ni bansaniba kawai abunda nasani aure nakeso kuma mansura zan aura dz oll

Dad yace how dare you ina mgn kana mgn to baxaka aure taba indae nine mahaifinka aure tsakanin ka da mansura babu sedae kuwa in wasu iyayen zaka canza , amma matukar uba ke nemar wa yayanshi aure , to wlh bazan nema maka auren mansura ba , ina auren yaya kaikuma zaka aure kanwa, bad脳 Ai abun yama kazanta wlh

Ahmed  yatashi afusace yace find dad, nikuma idan har ba'a auramun wadda nakeso ba, to wlh baxan yarda da auren kowace mace ba, kuma baxan taba aure ba har abada, dad yazare ido, son ni kake gayawa mgn ? Ahmed yace sorry dad amma idan har kadaga bazaka bani abunda nakeso ba to wlh zaka cigaba da ganin irin haka ni kawai abani abunda nakeso yana kae nan yafice daga dakin

Hjy dake labe tana jinsu tayi murmushin mugunta tace yauwa Ahmed aranta yana wucewa tashiga dakin, kamar bataji komai ba tace alh yana ganka wani iri ne? dad yace no bkomai kaina keciyo hjy tace shikenan idan taruba maji, dad yakalleta ya girgiza kai, sann yace ina bukatar hutu zaki iya fita, hjy tace basae ka koreniba dakai na zan fita, tafita dakin tana murmushi, tana isa dakinta tasaka Kiran mansura nan tazayya nemata komai

Mansura tahau ihu tace kae anty kice nakusa zama amarya wayyo dadi, hjy tace nadae gayamiki wlh kikama kanki kizama Yar mutunci, mansura tace hava anty sedai a rika sakayawa amma ko 2dyz baxan iya yiba ba'a yi abun nan ba, hjy tace kyaji dashi shegiya kinzama taxi motar kowa kowane kato hawanki yake, mansura tace no anty manya dae kinsan nifa nafison yara sunfi iya sarrafa ka dakyau, hjy tace dallah yimun shiru marasa kunyar banza idan dae kika je kika nuna masa maitarki afili kekika sani

Mansura tace inahhhh anty ay sekinga yanda nake kamewa amma wlh ina cike da kwadayin wann yaron zai yi cwet馃槝 sosae hjy tace tirrr da halinki kekam kinma guce harija idan da abunda yafi haka tokuwa kin kai can, mansura tace yp anty kinsan bana wasa da fruits dz y always akwai ni'ima har tsiyaya nake, hjy tabuga tasaki irinku ake rabawa aure idan kuka hadu da wanda baya iya daukar dawainiyarku, mansura tace kamm anty wlh baki saniba randa naja hannunsa zua dakinshi koh uhm..wani unexpected shock naji baki ji yanda nayi release ba nan take aranar kuwa koh.....har safe dreaming dinshi nake amafarki ma ya iya rolling din mace bare kuma afili kae I like him so so so much.....hjy tabuga dogon tsaki takashe wayar...........

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 5鈨�7鈨�
Dad zaune a dakinshi shida abba suna tattauna matsalar Ahmed, abba yakirasa yace komai kake kaxo yanxu kasameni a dakin mahaifinka, Ahmed yace ganinan xua dama yanxun na shigo wanka kawai zanyi se nafito, dad dajejin komai yace kagan rayuwar shi koh ace muna matsayin iyayensa muce shi muke jira amma yace se yayi wanka

Abba yadaga masa hannu ya isa bayadda muka iya dashi se addua tin haihuwanshi haka yake, Ahmed kuwa yana shiga dakinshi ya jona kettle yayi wanka yasaka jallabiya sann yasha eviron drink, kana yanufi dakin dad dinshi sallama ya musu sann yagaida kowa  yama kansa gurin zama, abba yace kasan meyasa muka kiraka, Ahmed yace no, abba yace gud, mgn ce akan auren dakace kanaso , nayi matukar farin cikin Jin wann zancen koba komai zaka zama babban mutum

Amma wani hanzari ba gudu ba meyasa kace mansura kakeso , bayan akwai yan mata tsaranka sann idan ka duba abun ta wata fuskar mansura antynka ce tinda kanwar matar ubanka ce bai Haram taba amma abun yakazanta, Ahmed yace gud abba tinda har kagane bai Haram taba toh bakomai nidae kawai auren nakeso kuma ita zan aura , abba yace katabbatar ita kakeso, Ahmed yace eh, abba yace shikenan zaka auri mansura matukar mahaifin ta yabaka ita, amma karka kuskura kaxo mana dawani zancen abaya komai yafaru after weeding dinku ba ruwanmu

Dad yace yaya meyasa zaka biyema ra'ayin sa to nidae ba daniba kuma bazan je neman aure ba gidan surikina, abba yace dama wayace kae zaka je ay ni zanje ba kunya tinda addini bai Haram taba  koh? Dad yace amma dae Ahmed kasan foundation dinda yake kasa koh? Ahmed yace banmantaba abba kuma baxan bijerewa hakan ba, nidae kawai abunda nakeso tinda nafaranta maka kaima kafaranta mun , dad yace hakane shikenan jeka allah yasanya alkairi yazaba mana mafi alkairi ameen , abba yayi murmushi yace ko kaifa

Ahmed yana fita yasaka Kiran mansura dama kuwa tayimasa 7 miss call yana kiranta bata wani Jan epixy ba tadaga wayar, hava bae tindazu fah nake kiranka, Ahmed toh sarkin mita zaki fara koh, mansura tace yi hakuri ranka yadade, Ahmed yace better yaushe ake samun ubanki agida, mansura tace bangane ubana ba, Ahmed yace ur father nake nufi, mansura tace shine zaka wani cewa ubana abun kamar zagi,

Ahmed yace toh yakike son ince inba ubanki ba, ko karya nayi ba ubanki bane? Mansura tace naji ya isa ubana ne, ko yaushe zaku iya samunsa sbd yadena fita outside sedai inza a duba lfy shi, Ahmed yace ban tanbiyeki wann ba iya abunda na tanbiyeki zaki  amsa ,mansura ta bata fuska kamar tana ganinshi ....nidae asea ina gefe ina dariyar  manya , Ahmed yace alright kigaya masa su  abba zasujo neman aurenki, what? Mansura tace kae wayyo allah nah, yaushe ne bikin dear nah, Ahmed yabuga tsaki yace wato har murna kike zaki bar gidanku koh?

Mansura tace no inadae murna zan je gidan habiby na hubby na my soul my gentle my......Ahmed ya katse ta keeee ya isa sarkin zuga zaki wani cika mun kunne da surutan banza, mansura tace au bakaji dadin kalamai naba kenan ?Ahmed yace yo wani dadin zanji acikin wann surutu kinwani wae my me my me 馃槒 mansura bawani kaedai dadi ne yakasheka, Ahmed yabuga tsaki ya kashe wayar, sann yakira Mahmud yace man akwae story fah kashigo gida yau,

Mahmud yace ina kan hanyar xua fah na biya market ne zan siyowa joda chocolates kasan akwaita dason chocolate, hello hello tasaki yabuga wato na dauko masa zancen makikiyarshi shine ya tsinke wayar , dae2 nan yakawo kasuwar chocolates kaday yashiga siya kala2 Seda yasiye kusan kala yakai goma se flower mai kyau da greeting card dauke da luv  quote 4 my 6 tareda tirare jidda mai shegen kamshi ..........

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
    馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
       馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
          馃巹 馃巹 馃巹
              馃巹 馃巹
                 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 5鈨�8鈨�
Joda zaune kan dakalin gidansu tana shan alawa 馃嵀 tana yan wakokin Justin B, driver dinta yazo yace barka da hutawa madam, joda tadago cike da girmama wa takarba, Yace madam kishirya xua 12 zamu fita dake , joda tace kamarya fita xua ina? driver yace kedai kishirya wann umarni ne daga oga nah, ga wann yamika mata wata pink gown, da pink shoes, sarka da yan kunne ma pink se wani katon ribbon pink, yanuna mata wani pic. kinga madam yanda kikaga wann baturiya haka zakiyi shigar shi plss karki bata mana lokaci oga ni zai yiwa fada ,

Joda tace nifa banganeba waye wann ogan ne, shiru tayi ganin yajuya yace mata no African tym madam, joda tayi tagumi a iya tinanin ta abdallah take zargi domin kuwa yasha gayama ta zakiga ina ta yimiki abu amma bazaki gane ya abun yakeba, murmushi tayi ta shiga daga ciki, tanuna ma gwaggo kayan gwaggo tace toh amma dae zakisa ka mayafi koh joda tace no kam gwaggo wann rigar ba'a saka mata mayafi ,

gwaggo tace gsky ba'a San raina zaki fita haka ba amma kije kishirya tinda yanxu kinga 11 tayi, ba musu tashiga wanka tana fitowa tasaka Kiran khalthum tace plss khalthum kizo kirakani wani guri yanxu2 ni ake jira , khalthum tace kamar ya yanxu nifa bacci nake kintadani,  joda tace plss khalthum kizo Dan allah nima bansan ina zamuje ba an kawo mun wasu kaya kamar wata india, khalthum ta kyalkyale da dariya wow kice party zamuje

Joda tace party kuma wae iskanci tona ubanwa zamuje nidae kawai kishirya, khalthum tace  wait kada ki tsinke wayar gaya mun wani irin kaya ne Dan nima nasan irin shigar dazanyi, joda ta zayyane mata komai, khalthum tace kambu allah har na hangoki amma pah simple make up yakama kiyi kisaka pink lipstick karki saka eyeshadow kisaka eyeliner white seki saka maskara ki gyara idon ki karkiyi brow , taki kullum kamar anyi shape  dinta  dae2 kawai kigyara ta da brush amma fah kisaka blush sae kinyi Dan smiling sann zaki shapa, joda tace ohh ni Yar fillo, naji Mrs make up,

Duk yanda khalthum ta zayyane mata haka tayi, tsayawa tayi tana kallon kanta ta mirror, tana murmushi ina hafsa ta itake son ganina haka aranta tace da inada camera danayiwa kaina hoto na ajiye mata, sallama taji anyi dasauri tajuyo tana dariya yayana kaine, Mahmud yabita da kallo duk yarude yana domin kuwa da batayi mgn ba bazai gane ko ita bace, gashinta yake kallo a iya sanin shi bata retouch or something like that, buh yagan yayi wani murde2 kamar anmasa wani abu se sheki yake babu abunda yafi burgesa irin yanda tayi parking dinshi atsaka takawo wann ribbon tasaka

Joda tace yayana mekake tinking haka? Mahmud yace no nothing kanwata nagan kinyi kyau ne waya koya miki dress da make up haka? kinsan allah idan kika fita za'a zata india ce, joda tace kae yayana bana san zolaya wlh, Mahmud yace allah, ungo wann wata irin jaka ce mai kyau, dasauri takarba tashiga budawa tirarika ne dasauran abunda yasiyo mata, tuni tashiga wangale baki nagode yayana kae naji dadi wlh, wata mp yabata tareda kunna mata wata romantic songs mai taken valentines day , joda takara rudewa yayana bansan mezan cemaka allah abun yaburgeni ashe Yaune valentines day inaji anafada a skull dinmu

Mahmud yace zomuyi selfie pics joda tazo dasauri Mahmud yadan matsa kadan yadda jikin su bazai goguba yafara daukan su pics,  ana haka Sega khalthum cikin wata gown itama tasha kyau dayake khalthum ma ba baya ba gurin kyau, sungaisa da Mahmud nan, shikuma yabasu guri, joda tashiga nuna mata kayan da Mahmud yabata , khalthum tace kaiii anya kuwa ba so" ana gurin yanda ma yake kallonki daban ne, kai amma pa ni kaina abun yaburgeni wlh

Joda mayyar chocolate tabude tafara ci, gwaggo tashigo tace lfy nakejin ihun ku , joda tace zokiga gwaggo ya Mahmud yabani, gwaggo tace iyye Yar yayanta kinsha godiya aykuwa ki kawo chocolates dinn inba haka ba kafun gobe duk kincinye shi  , idan watan Al_adanki yayi kice maranki keciyo bayan ke kekike cin kayan tsaki. ...........

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 5鈨�9鈨�
Joya ta bata fuska hava gwaggo nifa bashi yake sakani ciyo ba allah ne yake kawo mun,  gwaggo tace eh allah yake kawo miki amma ke kike kara wahalar da kanki , gwaggo takarbe chocolates din tasaka ajaka, tace keda sake cinsa se jibi, iddanana  ( kina jina ) joda tace Dan allah gwaggo munyu  ( kiyi hakuri ) kibani,  gwaggo tace bazan bayarba, khalthum tace gwaggo kara mata daya mana

Gwaggo tace ware ja'u  ( zo karbi ) joda ta gwaguda baki tace midamu wara  ( banason sa ) gwaggo tace kekika sani dae tajuya tafice tabar joda na kunkumi, dae2 nan driver yaxo yace madam time x over fah, joda taja hannun khalthum suka shiga motar tafiya sukayi mai nisa, sun hau wani sabon titi tsitt yake bakomai se kukan tsuntsaye kake ji,

joda tace wai ina zamuje ne ? driver yace sorry madam har munkawo fah , wani gate suka Parker wanda yasha mayun flowers , joda ta kalli khalthum tace badae nan zamu shiga ba, khalthum tace to ki tanbiyeni nace miki what? Joda taja hannun khalthum suka shiga driver yace bismillah madam, joda tace bangane ba kaifa, driver yace iya nan kadae aka bani umarnin na kawoki plss kishiga daga ciki ,

joda takalli khalthum, khalthum tadaga mata kae, suka shiga, khalthum itace ta iza gate din yabude , wani  kamshi da sanyi ya ratsa zukatansu  ji kake suna taka wani lallausan carpet , cak suka tsaya ganin danja takawo ko ina se ga wasu flowers dake xua daga sama joda ta daga kae tana kallo , tareda murmushi atake taji wani nishadi yana ratsata, khalthum tace joda kinga wani guri

Cake ne agurin mai shegen kyau babba ansaka happy birthday joda, joda tace wow hw cwet 馃槝 allah nama manta Yaune bithday dina, khalthum tace nifa narude wann surprise haka, daga ina? Joda tace oho nima bansaniba, shiru sukayi Jin waka na tashi ta happy bithday to you, joda tace ohh gosh, joda tace khalthum mu yanka cake din. joda ta yanka suka ci ga lemuka nan birjik, gakuma naman kaji, se su greeting cards sunfi biyar Dana valentines day Dana bithday ,

joda tace khalthum bansan mezanyi ba gurin nan yahadu ko ina mayen decoration ne akayi, komai na sukayi gurin pink ne, ta   zagaya gurin duk inda suka leka zasuga flowers da rubutu valentines day, ko birthday, khalthum tace kenan kekam a 14 February kikazo duniya, joda tace eh fah nazo ranar masoya gaba dae suka sa dariya  , khalthum tace zomu fara karanta cards dinn joda tace dayawa fah, khalthum tace ni zan karanta idan baxaki iyaba

Na valentines suka fara dauko wa, joda tace lah kinga wani littafi cikin leda yake joda ta yage ledar sann ta Zare flower din wani rubutu mai kyau da biro kam akayi shi amma yayi matukar tsaruwa ba mistake ko daya aciki , joda tafara karantawa  Sallama agareki tauraruwar zuciyata kece farin cikin rayutawa, kamar yadda taurari ke haske gami da kyalli asararin samaniya to haka fuskanki take haske famida kyalli acikin zuciyata

Khalthum tace wow bana Jin dadin hausa quote amma gsky wann yamun dadi,  joda tace nima fah , khalthum tace oya buda mana next page . joda tace to kinga wann da English ne, kezaki karanta mana khalthum tace ok bani nakaranta, joda tamika mata, khalthum tafara " 4u see each dy I luv u more 2dy more than yesterday and less than 2morrow so happy valentines day  " khalthum ta kalli joda tadaga gira ya kika ji wann, joda tace Muje next nidae khalthum tafara " life is a journey, so enjoy every mile happy birthday "

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B aleeyu 馃挄 page 6鈨�0鈨�
Haka suka ci gaba da karantawa har kusan 2 suna gurin sunma manta da tsawon lokacin da suka dauka agurin joda harda su cire takalmi, kwance sukayi kan carpet din suna karanta cards din idan joda taduba wann tabawa khalthum wann , Seda suka gaji Dan kansu suka kira driver yakaisu gida, badan ransu yasoba sedan kawai lokaci yatafi joda kam Seda ta ebo flowers din dasauran kaya ga uban chocolates da biscuits, khalthum kanta bata taba ganin irinsu ba

Khalthum aka fara saukewa itama ta ebi nata kayan sann tawuce, joda ta isa gida se faman cin chocolate take kafun su isa gida tacii biyar duk girman su , sadaf2 tashiga dakinsu taje taboye chocolate din kar gwaggo tagani takarbe, wanka tayi tacanza kaya, atampa tasaka riga da Zane tayi daurin Dan kwalinta oll back. Sann tayi sallan azahar da la'asar,

hasana tashigo tace joda Dan allah kimikawa su isa driver abuncin su, joda tace yana ina nifa tsokanar shi ce banaso, hasana tace hava dae kiyi hakuri ni yanxun cake zanfara toyawa waccan masifaffiyar kafun tazo tacimun mutunci, joda tasaka dariya tace gsky kam, kular tafara kaimusu sann takoma tadauko plates da spoons, takai musu , zata juya ne taji ance kamar yanda taurari ke haske gami da kyalli asararin samaniya to haka fuskanki take haske gamida kyalli acikin zuciyata,

joda tajuyo dakarfi abdallah dama kaine kayi haka, abdallah yadinga mata murmushi, Yace zomuje bae kigan wani big surprise , joda tace a gain kuma Zagaya yayi baya da ita yabude wata kofar sann yace rufe idon ki  tarufe kyalle yasaka yadaure mata idonta hannunta yaja sukayi Yar tafita sann taji kamar ansake buda wata kofar sekuma aka rufe, abdallah yakalleta yayi murmushi yace oya bude idonki, tana budewa taga flowers ko ina jajaye  bedsheets shima ja, tace wow ya abdallah amma nadazu yafi kyau shi komai pink ne, abdallah yace dazu kuma joda tace eh mana, abdallah yace ok naji yanxun ba wann ba mezaki bani as my valentine , joda tace mekake so

Abdallah yace duk abunda kika bani inaso, joda tace a'a nidae kafada kawai, abdallah yace ok ke nakeso, joda tace nima kai nakeso, abdallah yace kanki zaki bani koda 15 mnt ne, joda tace yo ay dama ni taka ce , abdallah yace ba wann ba ina nufin kibani jikinki na more ki koda na 15 mnt ne, joda tace nifa wlh banganeba , abdallah yace ok lamme proof it

" fuskanta yajanyo yafara shafa bayan ta jikinsa kuwa se bari yake " joda ta turasa da karfi abdallah mekake nufi ne  , abdallah yace plss joda just in seconds mun gama wlh zan miki ahankali, kwalla yacika idon joda tace abdallah dama Amma jikina kakeso bani ba, allah ya isa tsakanina dakai, kacuci Soyy ta kayaudareni

Abdallah yadaka mata tsawa ni kike kira da mayaudari, to yau zan nuna miki yaudara, yafara kiciniyar cire mata riga dayake zif ne har kasa baisha wata wahala ba yazare shi joda ta kankame jikinta tafara matsanancin kuka , kaji tsoron allah dadin da zakaji na kankanin lokaci ne yafita nikuma kagama bata mun rayuwa abunda iyayena sukayi she karu suna tanadi , wace amsa zanbawa mijina alokacin daya kusan ceni yajini ba'a cikakkiyar budurwa ba , wa'azi tashiga yimasa kota ya amma ina wanda yakauce hanya ya kauce kenan

Kanta yabuga abango tuni ta buga wata shegiyar kara yazare rigar takasance daga ita se vest, kuka take har muryanta baya fita kan gado yakada ita yahanye ta, tuni ta gan tsara masa cizo, Seda yayi Yar kara turasa tayi takoma kan ganbu zata bude, abdallah yataso dasauri yafizge key din yajefa a window yarufe , ganin haka yasaka joda buga shegiyar kara amma dayake sama ne suke ba'a ji sosae kan gado yamaida ta, joda kam ta sadakar rufe idonta tayi, tana adduar neman tsari........馃槶

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
    馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
        馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
           馃巹 馃巹 馃巹
              馃巹 馃巹
                 馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page6鈨�0鈨�
Kiss din wuyanta yake kamar zai cinyeta jikinshi se bari yake yagangaro abakinta joda ta rufe shi gam yadda bazai iya saka nashi ba, rigarshi yake kokarin cirewa dama kuma bx ne ajikinshi , yana kokarin zare wandon ne sukashi an wani irin hankado ganbu, abdallah yajuya dakarfi, 馃槼 Ahmed mekazo yi dakina, Ahmed yawankeshi da mari zai kara wata magana yasake marinshi janyoshi yayi yabuga kanshi a bango

Duka yake kaimasa ta ko ina seda yamasa lilis sann yace kajira sammaci akotu, Dan wlh sena bimata hakkinta, shikenan kawai kaga yarinya yar kauye zakazo mata da yaudara ke kuma yanunata......shiru yayi ganinta kamar a sankare hawaye na zuba amma jikinta baya motsi, dasauri Ahmed yadaukota se jijjigata yake amma taki koda tari sema kara faduwa tayi ajikinsa,

Ahmed ya azata akafada bai tsaya ko inaba se dakinki, kan gadonshi ya ajiyeta, duk yawani rudewa, dakyar yasamu yadauko jakarshi yahada mata allura, yamata aykuwa anan ake yinta, randa taga allura tafara motsi, Ahmed yabita da kallo da harara, juyata yayi baya zai mata allura amma me tajuyo da karfi ni wlh bana son allura kakaini inda gwaggo na

Ahmed yace gud tashi muje daganan sena gaya mata abunda kuke aykatawa keda Abdallah , joda tace Dan Allah karka tona mun asiri wlh baimun komai ba, Ahmed yace nidai baruwanka kijuya amaki allura, joda tarike gado gam, yana sawa tawani irin ajiyar zuciya harda su hawaye, tsaye tamike zatabar dakin sekuma jiri ya ebeta Ahmed yana kallonta yabarta tafadi akasa, sekuma tasaka mishi kuka, tuni yadawo real Ahmed, yadaka mata tsawa joda tace, dama yayan hafsa ne nazata ma ya Mahmud ne "

Ahmed yace wlh idan bakimun shiru ba zan hadaki da bango jikinta yadau rawa , tayi shiru Dan kwalinta tacire tadaura shi a kirjinta, Ahmed na kwalinta yabuga tsaki duk daya tuna irin yadda yasame Abdallah kan jikinta se wani bakinciki yaziyarci zuciyar shi , tsanarta kuwa tadawo masa sabuwa Joda tana son fita amma kuma taga yafita harkanta yakoma kan system yana ayki, lokacin sallah yayi

yafita xua masallaci yadawo yasa meta zaune se kuka take tana yiwa Abdallah Allah ya isa, Ahmed yace ke kimun shiru kafun na fasa bakinki ubanwa yakaiki dakinsa ay kina so din " joda tadago dasauri ni wlh cuta na yayi mugu azzalimi Allah yahadashi da bala'i da masifa, Ahmed yace kuttt nakara Jin kinma Dan uwana muguwar addua sena saba miki Joda tace ni zanfita inyi sallah Ahmed yamata banza yadauko abincinsa atake away yaci tareda soya milk, joda tasake maimaitawa nifa banyi sallah ba

Ahmed yaballah mata harara dole tayi shiru, seda tacire ran zai yi mgn sann taga yabude wadrop yadauko mata wani katon hijab yajefamata, joda tace ina ne toilet? Ahmed yace toilet din ubanki, kucaka dake katsama xaki shigarmun toilet wato kizubar mun da najasar dinda kika fitar koh " joda tashiga girgiza masa kai, yadaka mata zaki wuce kose na ballaki, joda tara ba, bayanshi tafita , har takai kofa yace jimana " tajuyo, dettol yajefamata zaki iya hadawa da warm water kizauna kar HQ din taki tayi xafi koh " sann ki tabbar kinyi wankan janaba b4 ki kusanci ubangijinki"

Joda ta aza hannu aka tafashe da kuka shikenan Abdallah yagama da ita , yacuceta, tafiya take se famar matse kafafun ta take gudun kar agane halin datake ciki, tana isa tayi sa'a bakowa tafada toilet tayi wankan tsarki sann ta hada ruwan zafi da dettol tazauna, kuka take kamar zata shide tana fitowa wani zazzabi yarufeta " kan gado tafada ko sallar batayiba, tafara kuka ciyon kaine mai tsananin gaske yataso mata har bata iya gani batajin zancen mutane sosae, gwaggo tashigo da nufin tadata tazo taci abinci amma kuma sae tasameta tana kuka kadan2 alamar tayi harta galabaita kenan,

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page 6鈨�1鈨�
gwaggo tace lfy "yan nan ? Joda tashiga nuna mata kanta, idonta arufe gwaggo tace subhanallah sannu joda, joda tace gwaggo mutuwa nakeso rayuwa ta batada amfani aduniya, gwaggo tace yau na banu ciyon kanne yafara gusar miki da tunani haka bara akirayo driver muje asibity , joda se nishi take, ba'a Fi minti biyar ba Sega gwaggo da hasana suka sata a mota sann sukayi asibity, dazuwansu suka hadu da wata aisha da suka sani I tace tamusu jagora xua ciki, aisha tace gashi nikuma lokacin tashina yayi amma bara akira likitanta tinda yace kome yasameta anemeshi

Doctor aysha takirasa amma yace bazai samu damar xua ba tamasa nasiha ta dubata dole badan tasoba ta tsaya tadubata , bayan tagama gawaje2 tace joda mesa jininki yahau? Joda ta gwale ido hawa kuma nima bansaniba, doc aysha tace shikenan Allah yasauwaka, tabata magunguna suka dawo gida

Zancen auren mansura da Ahmed  ya kankama , amma me jikin Ahmed yayi sanyi yakasa sakin jikin sa, bayan da har anbiya sadaki da kudin aure ansaka time wata mai xua, mansura kuwa anshiga gyara bakama hannun yaro, matsi take har na fitar hankali , magani ba'a daina yiba amma har yanxu Ahmed yaki zama yanda akeso

Tin ranar da abun ya faru joda batasake haduwa da abdallah ba kuma bata daina tsine masaba, abdallah kuwa yayi regretting yafi dubu, gashi based samu abunda yakeso ba gashi yarasa soyyr joda, kuka yake yi sosae yana alawadai da zuciyar shi, se yanxun yakejin sonta sabo na ziyar tarshi , ya daina fita ko ina saboda kunyar Ahmed da joda amma zuciyar shi takasa sukuni yana son gafarar joda koda zai samu nutsuwa aranshi

Yau tin safe yashirya yayi wanka yanufi kofar dakinsu joda ay kuwa yana xua segata zasuje skull, joda na ganin shi takurma ihu takoma ciki aguje, ganin haka yasa abdallah yabar gidan, hasana tafito aguje tana tanbayar lfy? Joda tace kunama ce nagani, hasana tarakata har mota sann tadawo neman kunamar bata gantaba aranta tace yanxu haka wani kwaro ne anma tace kunama, nidai asea nace eh yes kwaro ne amma babba uban kwari ba

Dae2 gate tahangoshi yadaka tarda driver, joda tace kai kadesa muwuce, driver yace hai madam sokike oga ya korani , joda tace okay budemun motar natari keke, yace wann kuma bazai yuba ki tsaya kiji abunda yakeson cewa mana, joda tabuga tsaki tajuya fuska , abdallah yakaraso yace plss kabamu guri zamuyi mgn, joda tace wlh idan ka fita nima fita zanyi dubifa 7:30 nayi late sosae, abdallah yace shikenan zan jiraki ki dawo koba komai naji sauki dalilin ganinki lfy lau

Joda tabuga tsaki zaka gama borin kunyarka kadena macucin banza wlh nafison ganin fuskar gorilla akan taka sautin zaki yafinaka dadi azuciyata, abdallah yace Allah yahuci zuciyarki, joda tacewa driver zaka wuce kose na ballah ganbun " kuji joda kamar wata kakkarfa " abdallah yabuga kanshi a bango yanxu gashi duk soyyr datake yimasa tarikida takoma kiyayya tsantsar ki nake hangowa a idonta , ya Allah ceceni

Ahmed yakira Mahmud yaxo akan suje zaba gidan daya masa a cikin gidajen dad dinsu, Mahmud se tsiya yake masa ango2 kasha kamshi nifa baxan yarda kayi auren nan bada niba, gwara nima na nemi tawa, Ahmed yace wann kuma kaitashafa, Mahmud yace nifa kanwarka tamun, Ahmed yadaure fuska wace daga ciki, Mahmud  yace D cute be dinn amina, Ahmed yace to badaniba jeka same ubanta, Mahmud yace kaima ubanta ne..........

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page 6鈨�2鈨�
Ahmed yace baruwana fa wlh yarinyar batada kamun kai you know agabanka nazaneta kwanan baya, Mahmud yace saimi toh iyakacin iskancin mace ace tayi cikin shege to so what " virginity dinta ba shine abunda nake bukata ba, in har tana sona zan iya canza ta daga mummuna zuwa kyakkawa, Ahmed yace lallae se yau na tabbatar baka San mekake ba

Mahmud yace kai bafa budurcin mace shine abun bukata ba obeying kawai indai zata mun da'a to wlh tafimun virgin dinda zataxo tana Ci mun mutunci, mu maxa se muce dole se virgin wlh watarana wata kaddara ce kawai wadda baka Fi karfin yarka" matarka" kanwarka" uwarka" tafada aciki ba , idan bama auren irin wadann matan lalaci bazai taba kaura ba a duniya , aurensu jahadi ne babba " kuma bana Jin auren irin wadda kakeso zaifi wann lada dakyar ma idan ba wann yafi lada ba

Ahmed yace ya isa Dan Allah el_sheek  , kazo kacikani da wani zancen banza kowa danasa ra'ayi kagane koh " Mahmud yayi murmushi yace Wanda yayi nisa baya Jin kira, dae2 nan suka kawo wani gidan , sun shiga ciki suna dubawa amma Ahmed sae complain yake yana kawo matsalar gidan,

Mahmud yace dakata malam wlh nagaji da yawon nan iskancin banza tin dazu muke yawon duba guri amma duk inda mukaje se kawo matsalar shi, Ahmed yace duk basumin ba ne , Mahmud yace gud saboda kagansu ne inba dad ba waxai tsaya tawa kamarka gida kuma har se kazaba, Ahmed yace karfa kafara zubamun bansan zancen banza

Joda sun fito skull itada khalthum, suna fira, khalthum tace joda ga nakin nan yaxo, joda tace plss kibarshi bashida ayki ne, khalthum tace tohfah yaukuma keda kanki, joda tace ehh kibarshi kawai munyi break up ne kuma wlh baxamu taba dawowa nomss ba, khalthum tace insha Allah joda har yanxu kina sonsa na tabbatar abunda yamiki bakai kimasa wann horon ba, joda tace plss khalthum bakisan abunda kefaruwa ba just leave me alone, plss khalthum tace shikenan Allah yasauwaka

Juyawar dazatayi taganshi agabanta idonsa tab dawaye yace plss joda karkiyi judging dina tahaka zuciyata bazata dauka ba, Dan Allah kisaurareni wlh tin randa kika shigo skull dinn nake jiran fitowarki banji yunwa ko kishi ba, ganinki da yafiyarki shikadai ne abunda nakeso arayuwata, joda tabuga tsaki tace abunda baxaka taba samuva har abada baxan yafe maka ba tana kai tajuya dakarfi tashiga motar suka wuce, khalthum dake kallonsu hawaye tab a idonta itama tajuya zata wuce abdallah yace plss kitayani bata hakuri, khalthum tace insha Allah batareda ta juyoba

Yau kusan kwana biyar currr abdallah nabin joda anma wulankancin yau daban na gobe da ban. yauma kamar kullum tafito daga skull, dasauri yaxo yarike mata wando duk yarame yayi baki, joda tace malam wai lfy kake neman taramun jama'a, abdallah yace joda ko ubangiji munayiwa laifi ya yafe mana bare kuma Dan Adam, joda tace ayya Wanda yasan Allah shiyake da wann sanin bakaiba, abdallah yaduka har kasa yace Dan Allah3 joda kiyafemun, hannu bibbiyu yasaka yariketa joda tawankesa da mayen mari

Duk jama'ar dake wurin seda sukaji kukan marin khalthum tazare ido gamida juyawa abaya, samarin makarantar suka yo kansu, wani daga ciki yace ke dabbar inace zaki dubi girman wann mutun kimaresa aganan jama'a bayan da duk wulakanta shi da kike a kullum bai miki ba se kin hada da zagi, joda tace ohh....kazo rama masa ne ? Yaron yace kuttt yarinya karki kuskura kigayamun rubbish wlh yanxun jikinki tagaya miki

Joda tace  bismillah shege kafasa,  yadagan hannu zai mareta dasauri abdallah dakansa yake kasa Yadago yarike shi yace kana tabata wlh jikinka zai gaya maka yaron yace yi hakuri bruhh ashema kaine, abdallah yace kasan nine? Yace eh ay abokin bruhh dina kake hafix, abdallah yasosa kai hakane jeka bakomai zan gyara lamarin , yaron yace sure bruhh gsky yarinyar nan batayiba Sam batasan zafin soba, abdallah yace anjiya jeka dae sae anjima,

Yana wucewa abdallah yajuyo fuskar sa adaure, yace joda Allah yagani na name gafararki iya abunda zan iya " kuma Allah yagani har zuciya ta nayi nadamar abunda na aikata, kisani baxan kara biyarkiba akan kiya femun , zanje nacigaba da rokon Allah akan yasaka miki jinkaina kiyafe mun , koda bazaki soni ba burina kawai kiyafemun, amma kisani daga yau duk abunda yasameni kece ko yaushe zuciyata zata iya bugawa ayadda nakeji dinn bana tunanin zankai safe da rayuwa,

idanma har narayu to kuwa nasan se an gwammace mutuwata akan rayuwana yana kai nan yajuya yabarta atsaye tana hawaye.........

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
    馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
       馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
          馃巹 馃巹 馃巹 
             馃巹 馃巹
                馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page 6鈨�3鈨�
Wani gida aka Ahmed yazaba ba nisa da gidansu dukda bai masaba sedan kawai yanada side dinda yakeso, tini aka shiga gyaran gidan, hjy tazo tasame Ahmed da dad a palor , tace dama kunake nema, dad yamaida dubanshi a kanta, Ahmed kuwa ya cigaba da rubutunshi, tace alh dama nace kaida Ahmed waxai hado lefe ina nufin kai zaka masa ko kuwa shi zaiyi abun shi,

Ahmed yakalli dad ya girgiza kanshi, dad yace kamar wann zanmasa komai yanada abun shi shizaima kanshi lefe, hjy tace toh Ahmed wai dama nace kasan mata sunfi sanin abunda yadace , shine nakeson ka kawo kudin se muje dubai muhado komai nida amina, Ahmed yace dakata kinfi kowa sanin bana son shishshigi  alamurana, nizan hada abuna bana bukatar kowa yasaka mun hannu aciki yana kae nan ya ajiye biro dinda yake rubutu dashi kan table yafita a dakin , hjy tarakashi da harara

Ciyo mai tsanani yakama abdallah yarufe kanshi adaki bawanda yasan halin dayake ciki, amina ce talura kwana biyu baya fitowa breakfast, tayiwa hjy mgn, hjy tace waya sani ko yana can gurin iskancin sa ba mamaki ba ace baya gidann tin shekaranjiya, amina tace anya bruhh baya kwana biyu ba'a gida ba bara nadubo shi, side dinshi tanufa, tamurda ganbun atake kuwa yabude, kara tasaki ganin shi akasa yana murde2 da alama cikinshi keciyo

Dasauri takoma tasanadda hjy, hjy tin a dakinta take ihu da kuka, koda su kazo yanata kwara amai, dasauri hjy takira dad tasanadda shi, ba'a Fi minti uku ba se gashi tareda Ahmed sukazo aka saka shi a mota se asibity , ana xua Ahmed yakira wani likita suka shiga tare aka basa taimakon gaggawa, atare suka fito, Ahmed yace kamusu bayanin abunda kedamun dansu, likitan yace ulcer ce tamasa mugun kamu har zuciyarshi tafara ciyo, da alama yau sati daya baici abuncin kirki ba Wanda zai Gina masa jiki

Hjy tace shikuwa meke damunsa har dazai kauracewa abinci, dad yace ay laifinki ne kina matsayin uwarsa ace yadaina cin abinci amma baki lura da hakan ba wann ke nuna cewa baki kula dasu yanda yakamata watarana seya mutu bada sanin kiba, amina tace dama kasan koyanxu nice na lura yade na fitowa, Dana mata mgn cewa tayi kila baya gidan danabi takanta sedai muji warin gawarshi, dad yace kajiko, hjy tace kaji munafukar banza wlh sena ballaki sgegiyar yarinya kawai, Ahmed yabuga tsaki yaraba tagefen su yawuce

Kwanan shi 7 sann aka bashi sallama ko yaushe damuwa fal aranshi, joda kuwa tin ranar bata kara saka abdallah a ido ba , khalthum kuwa tayi tamata fada akan bata kyauta ba, joda dae jinta kawai take Dan batasan meke faruwa ba , sun fito exam yau tin 12 suka dawo gida dae2 kofar gate tahango abdallah yana tafiya shikadai amma se hawaye yake joda ta tsaya tana kallansa jikinta duk yayi sanyi shikuma kamar an ce yadago yahaganta, tana kallansa dasauri yakaraso zaizo gurinta, ganin haka yasaka joda juyawa dakarfi tareda bata fuska

Abdallah yace joda idan baki ya femun ba banga amfanin rayuwa taba, mota na xua gurin shikuma abdallah yatsaya kan titi, kiyyy!!! Kakeji dakarfi tajuyo tareda aza hannu aka tayada jakarta tana wayyo Allah, jijjigashi take amma ko alamun motsi ba yayi , se jini ke fita , duk ta haukace se ihu take da gudu tashiga cikin gidan, gefen garden ta hango Ahmed dasauri taje gurin shi tana haki

Ahmed yajuyo Jin ana xua aguje, jaridar hannun shi ya ajiye, yana kallonta jikinta duk jini ne " kanshi tafada tana kuka, yayan hafsa, mo...mo....tahhh.....ce takade shi baya motsi ya mutu, Ahmed yace waye dallah ki daga mun shegiyar yarinya , se a lokacin joda talura da tafada ajikinshi.........

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page 6鈨�4鈨�
Atare suka fito da Ahmed waje se kuka take tana fadan na shiga uku, Ahmed ya daka mata ki koma cikin gida kafun na halaka ki wlh kokuma se kin taramun jama'a , joda tace yazan koma navarshi ajikin wann halin " Ahmed yace gud karkije wlh idan nataso se jikinki tagaya miki dajin haka takoma ciki, aguje tafada kan gwaggo tana sanadda ita abunda ke faruwa

Ahmed kuwa motarshi yadauko yajashi sukayi asibity, dazuwansu aka karvesa emergency, seda aka masa dress aka sakamasa drip sann Mahmud yace yakira yasanadda su halin da ake ciki, hjy kam tayi ta masifa akanme Wanda yakedasa bai tsaya koda hakuri ya bayar ba, dad najinta yamata banza, abdallah kuwa ciyon zuciya ne yakamashi bayan da jininsa ya hau sosae ,

Ahmed yatasashi agaba seya gayamasa abunda kedamun sa, abdallah yayi shiru se hawaye yake, dad yace wai bada kai ake mgn ba, abdallah yace ba abunda kedamun sa , Ahmed yace wlh karya kake wani dalili ne zaisa ka kulle kanka har kwana biyar baci basha, ina hankinka yaje da har mota ta kadeka , tunanin me kake meka rasa arayuwa , dae2 nan joda tashigo ita da hasana, ganin joda abdallah ya kirkiri murmushin dole yana kokarin tashi, Ahmed da dad suka maida kallon su ga kofa Dan ganin meke faruwa, joda ta karaso tagaida dad da hjy dad ya amsa ciki da fara'a , hjy kuwa tabita da yatsina , abdallah yanunata yace itace itace dad wlh itace ciyona nasan na mata laifi na nemi gafarar ta har kasa naduqa na nemi, gafararta amma Sam taki Dan Allah dad kace taya femun

Hjy tace what?  Kaduqawa wann al majirar uwarta ka kashe ko ubanta? Dad yace ke dallah kimun shiru, joda gaya mun meke faruwa, joda tayi kasa dakai tayi shiru dad yace kigayamun idan cutar ki yayi wlh zan bimiki hakkinki, abdallah yace dad naso na bata rayuwar ta amma allah baisa nayi nasara ba plss dad, tayi mun kowane hukunci amma banda takini wlh idan ban auretaba gwara kawai na mutu

Hjy tace kuttt馃槨 wlh kar in kara Jin wann mummunan zancen wazaka aura din wann baran namu dasuke under mu, never wlh bakaxa taba auren taba kwarya tabi kwarya, dad yace ke kifita daga dakinnan kafun inyi mummuna saba miki, dad yamaida kallansa ga joda yace joda hakane yaushe kuke soyy da abdallah banda masaniya ? Joda tace tin bayan rabuwarmu da yasir, dad yakalli Ahmed yaga shi yake kallo, yace Ahmed kasan da wann zancen Ahmed yace no nima dae yanxu naji cos bantaba ganin su suna tadi ba

Abdallah yace bruhh Dan Allah kashiga lamarin nan nidae so nake aha da auren nan da naka idan ta amunce, Ahmed yace ke kina sonsa ne " joda tarike hasana kam atake taji kanta yayi nauyi wani irin sanyi yafara ratsa ta sekuma taji takasa fada tanaji aranta kamar akwai wani abun datake son fada amma kuma takasa, Ahmed yadaka mata tsawa ba dake nake ba, dad yadaga masa hannu yace kabita a hankali yarinya ce karama, joda tafashe da kuka, dad yace yi hakuri haka yake kinsan soldier se a hankali

Joda takaras kusaga abdallah tarike masa hannu ba hasana ba hatta dad da Ahmed seda abun yazomusu abazata ga badai suka samata ido " joda tace abdallah zan aureka idan kabi sharuddana  , zaka dena shaye2  da xua club, zaka daina bin mugayen abokai , karika bin umarnin iyayenka kazama kamilin mutun gentle kamar.....takalli Ahmed da gefen ido Ahmed ya balla mata harara, joda tace kamar ya Mahmud. Abdallah yace shikadai ne joda wlh zanyi na tabbatar ke alkhairi ce agareni, tin farkon ganina dake nake tsoron kiganni a maye abunda bana tsoron kowa yagani

Abdallah yace dad abamu sallama naji sauqi, dad yayi murmushi yakira doctor, doctor yace yanada yamike, ana auna bf dinshi a kagan yasabko sosae, doctor yace woww wae menene sirrin ne " abdallah yanuna joda yace itace ciyon itace magani, joda tasadda kanta kasa, dad yace lallae joda kinyi abunda muka kasa akai tsaye wato raba abdallah da shaye2, ha kika banida bakin gode miki, joda tace dadyn hafsa idan kayi mun godiya kayi haramun, nice yadace a koda yaushe na gode maka abisa dukkan alkhairan da kake mun

馃巹  FULANIN DAJI 馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page 6鈨�5鈨�
Ahmed yabuga tsaki yace kusameni a waje idan kun gama, dad yace bawani zama zamuyi ba kutashi muje gida , kayansu suka hada  sann suka fito, joda na makale da hasana suka fito driver dinsu nanan suka shiga motar har abdallah yabisu hjy tadaka masa tsawa, dole yadawo yabisu dad

Suna isa gida hjy takira mansura tazayyane mata komai mansura tace impossible, yama za'ayi abdallah ya auri yan DAJI Sam baxata sabuba, wlh kiyi gaggawar jamusu kunne, hjy tace toh yanxun makuwa, tana tsinke wayar, tanufi sa shen su joda , duk Wanda yaganta seya Duka ya kwashe gaisuwa amma ko kallan banza , tana isa taci karo da gwaggo, tace ke kuma matsiyaciya  ina gargadinki daki jawa yarki kunne akan tarabu da Dana wlh har abada Dana bazai auri yar matsiyatava,

dangin tsiya, gwaggo tace Allah yahuci zuciyarki, zan jamata kunne Dan Allah kiyi hakuri , hjy tace oho dai kinji nagaya miki idan bahaka ba wlh zakuga tashin hankalin dabaku taba gani ba arayuwa In banda kwadayi ina abdallah ina wann kucakar duk yaushe ne kuka dena tsoron mutane, wato ansata a makarantar manya ta waye ko,  to ahirr dinku zata juya kenan Sega joda, joda naganinta takoma aguje dasauri tacakumo wuyanta tace munafukar banza munafukar wofi wato kun shanye mun da baya ganin kowa seke harda wani gindaya masa sharudda koh "

ku kiyayeni fah, ta ture joda tafita tabar dakin, gwaggo tabi joda da harara kinga abunda nake jimiki koh mutunci yafi komai  yanxun gashi anci zarafinmu harda ubanki dayake kasa, ina amfanin hakan , mema zai saka kiyi sarakuta da wann masifaffiyar matar  , kikama kanki wlh idan bahaka ba abunda zasu mana agaba seya Fi wann , joda kam se famar kuka take

Tin a ranar  abdallah yamutsu yade na duk wani abu mara amfani dashi ake sallar asubah hasalima kowace a masallaci yake yinta, yamaida qur'ani abokinda carbi abokin firarshi, ita kanta hjy shi taji dadin yanda yakoma barinma dataji dad  yace zai basa day an company dinshi na sarrafa fata , Ahmed kanshi na mamaki aranshi kuwa yace Allah rabamu da masifar so " nidae asea nace ameen " so fah badama"

Soyy kuma se abunda ya cigaba sedai aboye suke yin abunsu, joda kam jitake kamar inba abdallah bazata iya rayuwa ba, khalthum se tsokanar ta take dama a naso ana kaiwa kasuwa , joda tace naji dae kema zan rama watarana ay, haka abun yake tafiya bawani takuri duk yanda hjy tasaka musu ido takasa gano su, amma wani gefen tana cewa hegiyar yarinya tamana rana tinda tarabashi da shaye2 yanxun ne yakamata na ne masa auren yar commissioner wato safina, toh fah

Ahmed dae sae shirye2 zuwa dubai ake hado lefe duk yanda mansura tayi dashi yaje da ita amma firr yaki xua da ita yace zasuje after weeding dinsu, mansura tace ok dear kabani key din dakinka kafun kadawo, Ahmed yace kajimun rubbish akan wane dalilin zan baki key din dakina, mansura tace gyaramaka zanyi idan zaka dawo, Ahmed yace kibarshi ngd, idan nadawo zaki gyara, fushi tayi tabar masa dakinshi , Ahmed kam ko a jikin shi danko bayau suka saba ba itake gajiya tadawo neman shiri

 Joda tafito xua skull ba driver dole ta tsaya cike da mamaki Dan baisaba hakan ba, tana tsaye hannunta rike da textbook tana dubawa, kamshinsa kadai yaganar da ita waye, joda tace doctor kaine da sassafennan, doctor yace eh wlh wata patient naduba nan bayan layin nan  , zan wuce na hangoki zo in rage miki hanya ba musu joda tashiga suka dau hanya, can yakira sunan ta, joda antaba gayamiki kinada kyau? Joda tayi murmushi tace tosaunawa ma , doctor yace amma fah ni wlh bantaba ganin kyawunki ba hasalima muninki na firgitani fari se kace yar aljan, joda tayi Jim tace nagode amma plss zaka iya saukeni anan, dasauri yade na kallonta sbd dariyar da yaxo masa

Yace yi hakuri fah gsky nake gayamiki wlh su basu San kyau ba, amma dakinga matata koh wlh sekin raina kanki fara se ba irinki ba ke komai nata fa special ne " joda tace koxan iya ganinta? Doctor yace tabb banaso irinku munana kuna hada hanya da ita sbd tsaro amma ke kanwata ce zan baki tym dae2 nan suka kawo skull din........

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
    馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
        馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
           馃巹 馃巹 馃巹
              馃巹 馃巹
                 馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page 6鈨�6鈨�
Tin ranar joda tashiga tinking kullum hanunta rike da madubi tana kallon kanta, aranta kuwa cewa take kila dai kowa kallon mai kyau ake mun shi isa ake ganin kyawuna, amma shi yaganemin gsky, sundawo daga islamiyya, tadauki tell phon takirashi , bayan sun gaisa  take cemasa plss doctor yaushe zaka kaini gurin matarka, yayi dariya sann yace bayauba kam inada ayki sedai ko zuwa jibi, idanma nasamu tym dakaina xanxo in daukeki inkaiki gurinta

Joda tace Dan Allah kada adauki long time wlh na kagu naganta, doctor yace ayku dama mumuna jikinku har rawa yake kugan masu kyau, sukuma masu kyau yan hutu ne " itama komai batayi daga skull se bacci fatarta kamar auduga idonta kamar madara bakinta kamar na jinjiri, dimple dinta tamkar na pretty , yatsunta zara2 doguwa ma'abuciya tsayin wuya, hips da boobs kuwa yanxun suke ta sowa amma abun se Wanda yagani,

joda tace nidae ya isa duk wann abun ace mutun daya aiko hurul'in ce iyakacin kyanta kenan, ita kenan komai nata indeed be batada miskila ko kadan aikam baxai yuba , doctor yace alright idan kin ganta zaki tabbatar da hakan, joda tace to ay nagama kamar rowar ta kake, yace ba dole ba saboda irinku karku sakamata asid a fuska, joda tace uhm...gamu gani dae

Karfe 7:30 nasafe jirgin Ahmed yace yadaga xua dubai , kafun yaje seda yajawa masu aykin gidanshi kunne kafun yadawo komai ready. dukda yadamka komai a gurin Mahmud , mansura awaya tana soyewa da wani honorable, yace hava sury wlh kinsan ina cike da kishirwarki Dan Allah kibari muhadu, mansura tace kaga honorable wlh nafara matsi ina tsoron ka lala tamun shiri gaka in kafara se mutun yaci uban shi kamar Wanda yakama wani nono

Honorable yakyalkyale da dariya, to ay kece tamkar Zuma wlh bantaba ganin wadda takaikiba kuma bakya tsufa, yanxun dae zanbada , 1m mansura tace dagaske, yace sosae ma kuwa kedai kawai kisama time, mansura tace gove dama fa nima amatse nake wlh sati daya babu abuncin zuciya 馃槀   Allah ka shirya su mansura ameen "

Joda suka hada appointment da abdallah akan zasuje kasuwa su siyo littafan addini, tareda wasu ababen, haka kuwa akayi dakanshi yajasu suka fita bayan tacewa gwaggo gidansu khalthum zataje, yar karamar market ce sukaje, sunsiyo littafai da dama ya kuma kwaso mata chocolate da cake, dae2 wani hotel suka gameda mansura tana rike da hannun honorable, abdallah yaja tsaki Allah yashirya anty sura, itakuma duk tagansu anma se tayi kamar batagansuba , wayarta tajawo takira hjy tashai damata  sann takira Ahmed

Ahmed yace toni ina ruwana rayuwar shi ce , nahanashi soyy ne " mansura tace to yarasa waxaiso se wann kucakar yar village, Ahmed yace oho tsakaninku ni kinka karki kara kirana in har kinsan soldier tsegumi zaki kawo mun, mansura tabuga tsaki ta kashe wayar tace Dan iska goma aka kawo maka mgn seka gwalashe mutun , abakin gate suka hadu da hjy taci damara se huci take kana ganinta kaga bala'i, tuni jikin joda yafara rawa tace Dan Allah abdallah saukeni anan, abdallah yace y" joda tace nidae bakagan hjyr kubane, abdallah yace naganta menene toh

Joda tace Dan Allah abdallah " banza yamata seda yashiga har harabar gidan, hakan yakarawa hjy haushi, ta dososu dasauri, tana nuna joda ke Dan uwarki bana hanaki hulda da Dana ba, abdallah yace ni zaki hana hulda da ita domin sena kulata take kulani, hjy kamun shiru mutunin banza , ke kuma tanuna joda wlh wlh wlh nawa uku koh idan naqara ganin ki da dana to kikarasa sauran zancen kawai

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page 6鈨�7鈨�
Joda kam tashiga dakinsu aguje tayi sa'a gwaggo na bacci, abdallah kuwa palor yashiga se wani huci yake, wayarshi yaciro yasaka Kiran mansura tana dagawa yace to munafukar uwa nizaki hada da uwata koh " Allah dae yasaka ba fasikanci akajimu munayi ke kuma gaki nan ansaka rana amma kina yawon dadiro wlh idan kika karamun haka sena dauki duk wani move naki nakaiwa Ahmed se inga abunda zakiyi dake har antyn taki marasa tarbiya da tsoron Allah kawai,

Mansura tayi sororo rike da waya lallae dole adaukarwa abdallah mataki idan bahakaba zai bata mata shiri, sann bazai taba auren joda ba wlh watsatstsiyar banza,

Lefe naji nafada Ahmed yayi tsayawa ma fadansa bata tym ne kawai ku kissima abun aranku, hafsa ma haka yahada mata nata Dan karamun lefen abun gwanin sha'awa, Mahmud kuwa yayi tsayin daka akan gidan Ahmed dukda yace agyara kowane side, haka kuwa akayi ko ina an gyara side hudu ne har gefen yara gidan ba'a cewa komai, daga India yasaka akayomasa order takaya ga baki daya su suka tsara masa parlor dinshi dakuma room dinshi sekuma wani dakin da'a ka gyara abun dae se Wanda yagani duk wann hidimar Mahmud ke yinta Ahmed yana can dubai , yana hado lefe

Abdallah yasami dad dinsu akan zancen joda yanaso anemamasa auren ta , dad yace abdallah bayanzu nakeso kayi auren ba nafison seka kara nutsuwa tukun sann kafara aykin company dinka gadan2 kaga a lokacin zaka iya rike iyalanka kome kace? Abdallah yace banida zabin daya wuce zabin iyayena dad duk yadda kayi dae2 ne aynasan bazaka cuceni ba, dad yace sosae ma kuwa son Allah yamaka albarka yatabbar da farin ciki arayuwarka Allah yasakawa wann yarinyar data zamo silar shiruwarka ameen " yana fita dad yacire glass dinshi yafara share kwalla, tausayin dansa fall aranshi

Mahmud yaxo gaida gwaggo kuma yasha fura, yakuwa yi sa'a anyi furar kusanma kullum se anyiwa dad furar, gwaggo tacikamasa kofi yana sha yana zuba santi, joda kuwa se dariya take masa, Mahmud yace idan kinamun dariya zangayawa matata tabaki Duka, joda tace lah ya dama kanada mata bansaniba, a nuna mun ita nagani, Mahmud yace kambu ayganinta se an shirya yarinyar tayi tsada dayawa , joda tace nidae ya Mahmud kaki ka kaini inda mom dinka, Mahmud yace kinshir yanxu? Joda tace eh ashirye nake, Mahmud yace ok dakko mayafinki kizo mutafi, joda tabuga tsalle bara na yiwa gwaggo sallama

Har zata bude mota taji ance yaukuma se ina naga har wani rawan jiki ake, murmushi tayi tin kan tajuyo tasan abdallah ne " gidan su yah Mahmud zanje in gaida momy sa, abdallah ahhh.....wann yanada kyau, se andawo Allah yakiyaye hanya, yadagawa Mahmud hannu bruhh Allah yakiyaye, Mahmud yace ameen bruhh, abdallah yace wait bruhh akulamun da matata fa kar abi hanyar duwarwatsu da ita , Mahmud yace okay kamanta tana tareda yayanta ne ' abdallah yace hakane se andawo

Tana shiga yatada mota, amma kuma me yanayin sa gabaki daya ya canza , joda tace ya lfy naga kadan canza, Mahmud yace bakomai joda kaina yake ciyo, joda tace ayya yayana Allah yabaka lfy, joda tadakko wata game acikin motar tana bugawa se murna take idan tacinye idan kuma aka cinyeta seta bata fuska, Mahmud dae yana kallonta ta glas sedai yayi murmushi amma shikadai yasan iya adadin son dayake yiwa joda amma yakasa fada mata yanagani kamar baxata dauka na amma gashi abdallah yakowa mata sonshi ,

joda tace lah ya Mahmud mekake da dettol acikin motar ka? Mahmud yace kinsan ko yaushe bukatar shi yana tashi, kuma x gud ma ace ollwyz kana tareda shi koda bukatar shi yaxo , tayi shiru tana tuna wata maganar da doctor dinta yamata abaya yana cewa x gud ki rika yawo da tissue kokuma pad , period dinki batada tabbas koda bukatar hakan yana tasowa, A'a confuse yana ji zancen yaxo iri daya, joda kam ta tabe baki tace anyway dae nasan su manyan maxa tsarin su daya ne

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page 6鈨�8鈨�
Atare suka shiga a gidan Mahmud yana gaba tana biye dashi, joda se bin gidan take da kallo aranta tace ashe ko ya Mahmud Dan maikudi ne amma baya nunawa kome yasa " Mahmud yace zonan, wata kofa suka bi segasu awani lungu yace nan kofar parlor nan kuma idan kika bi hanyar dakin abba da momy ne inazaki fara shiga,

joda tayi shiru tace ya Mahmud kafini sanin dae2 mana, Mahmud yace ok shiga parlor ina xua nayi mantua a mota ,joda tace idan na shiga Ince ni wacece,? kawai zan jiraka , Mahmud yace joda baki saba yimun musuba, meyasa zaki fara yau , joda tace yi hakuri ya Mahmud bara na shiga yajuya yakoma itakuma tashiga cike da tsoro2 sallama tayi tinda ga kofa tayi sa'a Shakur nakusa ya amsa sallama

Joda tashiga daga ciki tazauna se bin shakur da kallo take kamarsu daya da Mahmud ana haka Sega shukra, tazo tace lah baquwa muka yi wuce daga ciki, joda tabita har cikin palor, ruwa da lemu takawo mata sann tace bara na kira miki momy, atare suka dawo da momy, momy ta tarveta da fara'arta tana tanbayar ya gida yakowa da kowa, joda tace duk  lfy lau suke shukra kam se makalewa joda take tana janta fira  , can dae momy tace yasunan ki, tace joda, momy tace kiyi hakuri fah banganekiba

Joda tace tare da ya Mahmud muke yana waje, momy tawa she baki iyye ashe sarakuwata ce, shkura tabuga tsalle, takwalawa shakur kira, zo ga matar bruhh, joda kunya yakamata tadukadda kanta kasa momy tace shukra jeki kawo mata abunci, joda tace a'a nakoshi, momy tace ba'a yihakaba shukra kuje dakinku se taci acan kafun yashigo , har suka shiga taci abuncin tayi sallah Mahmud bai dawoba seta fara tunanin kodai tayi masa laifi ne

Shkura taja hannunta sunkoma parlor, suna tsakar kallo a system Sega shi yashigo, shukra tace bruhh matar nan taka akwai kunya wlh, Mahmud yace zanci ubanki wlh ita tagaya miki matata ce ko ni?  Momy dake saukowa downstairs tace indai taruba maji, Mahmud yace look mom wann fah kanwata ce, mom tace ayshi so dama yafi dadi idan akatafi dashi ta hakan , zallar so gashi a I donka kana wani boyewa, gara dae kasanar da ita kar kamun asarar sarakuwar kirki

Mahmud yace joda tashi muje gida, joda tayiwa momy sallama, shukra kam ansha magiya akan Mahmud yabar mata joda har xua night amma yaki sema zaginta daya fara yi , joda kam duk jikinta yayi sanyi haka suke tafiya amota kowa da abunda yake kissimawa aranshi, sunkai wani shago ya Parker yace me za'a siyamiki ixecrem ko chocolate, joda tace ko daya ba naci, Mahmud yace shikadai yajuya motarshi suka isa gida, sunfi minti goma da kawowa gida amma bawanda ya fito

Dakyar joda tabude ganbun motar amma kuma seta kasa fita , a hankali har muryarta narawa tace ya Mahmud dagaske ne abunda momy tace, yah Mahmud dama kana sona amma baka taba nuna munba , Mahmud yace joda ki shiga ciki zamuyi mgn ltr, joda tamike se hawaye take shikuma yajuya motarshi  , jodaaaaa nahhhhh. ....taji ankirata dasauri tajuyo Jin muryar hafsa,

da gudu ta sheka tarungumeta, tana hafsa na yaushe kika dawo, hafsa tace bajimawa, kinsan ankusa auren ya Ahmed shine naxo biki Allah ma yasa muna hutu, joda tace aure kuma nikam banjiba, hafsa tace kamar ya gaki acikin gida, next week fah za'a fara bikin joda tace lallae ma ashe kunfitadda anko, hafsa tace eh munyi waya da amina tace anfitar amma zamuyi namu daban kinji, joda tace Allah yakaimu tym din........

Like 馃憠馃徎@ RUNBUN ASEEYAH BASHEER fb. Com  zaku samu complete FULANIN DAJI 馃巹
Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
    馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
       馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
          馃巹 馃巹 馃巹
             馃巹 馃巹
                馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page 6鈨�9鈨�
Hafsa da joda ne tafe suna fiarar yanda bikinsu zai kasance, Sega amina tazo wucewa takira hafsa zo muyi mgn, hafsa taja hannun joda suka tafi, amina tace ke kuma ubanwa yakiraki nagadai yar uwata nakira bakeba, joda tace hafsa idan kungama kyasameni aciki, hafsa tace to shikenan Dan Allah kiyi hakuri, amina tace iyye wato ma hakuri kike bata, yanxun dae bama wann ba, Allah kada kije mana da ita abikin bruhh in bahakaba wlh se in diz gata a bainar jama'a

Hafsa tace akanme nagadai itama ta zama tamkar yar gida, amina tace to shikenan zaki gane wann shegiyar yarinyar dakyau kamar aljana ay se gabaki daya hankalin samarin yakoma kanta, hafsa ta kyalkyale da dariya, to kindaiji abunda zakije jealously kawai, amina tace wlh  zan jimiki ciyo mezanyi wa wann banxar kishi akai, hafsa tace ay sedai kiyi amma joda kamar taje biki ne ashobe bawanda ban mata ba  , hakama head ba abunda zaki nuna mata inmadai bakiyi hankali ba tafiki haduwa domin make up artist zan dauka har agama biki, amina tace bura'uba wlh se in gayawa bruhh nasan shi baxai bari aje da ita gurin bikinsa ba

Hafsa tajuya tareda Jan tsaki tayi gurin joda, koda taje tasameta suna dama fura da gwaggo, joda tace hafsa zoga fura ke nake damawa, hafsa tace kai my joda naji dadi wlh, joda tace hafsa plss kirakani gidansu khalthum inkaimata ankon nan , kartayi fushi dani, hafsa tace ok yaushe zamuje, joda tace bayan sallah magrib driver nakaimu seya dawo damu, hafsa tace toh shikenan Allah yakaimu lokacin joda tace ameen " gwaggo tace hafsa ungo wann ta abbanmu ce kije dakinshi kisaka masa a fridge amma fa karkibari yayi kankara zai lalace, hafsa tace lallae ma dad, yazarce da shan furar gwaggo, joda tace kinsan me, allah duk randa ba'a masa wann furar ba dakanshi yake xua tanbaya kuma wae duk wann plastic din kafun gobe yakare, hafsa tace uhm aikam dad zai iya yanaso fura ne sosae

Agidansu khalthum se tsokanar joda take tana cewa matar abdallah, hafsa tace nifa banganeba wane abdallan, khalthum tace yayanki mana shiyake son joda harda ciyon so yayi, hafsa tace iyye shine ba'a gayamun matar yayana ashe zamusha liki jibi , joda tace kinga hafsa banaso ki dena, hafsa tace tab aikuwa yanxun ma nafara kice munada shagali agaba mune yan amarya mune yan ango, kaiiiii abun zai bada ma'ana......shiru tayi ganin joda na hawaye, khalthum tace lfy joda? In dae kan wann mgnr ne to mun daina tinda bakyaso, joda tace a'a khalthum bashine abunda yasakani kuka ba,

Hafsa tada fata to menene joda, hawaye dake fuskarta tagoge sann tace hafsa wlh inason ya abdallah kodan shiruwar da yayi aka ina amma nasan niba matar bace inaji ajikina kamar ankusa rabamu dashi, hafsa tace wakuwa zai rabaku bayan da kunason junanku, joda tace a'a hafsa hjyr abdallah tayiwa gwaggo dani kaina garfadi akan danta, gwaggo ita kanta ta gayamun bata son ganina da abdallah takaras he zancen cikin kuka

Hafsa tace clm dwn, joda addua zakiyi kowane aure se yaxo datashi gaddama wani yaxo dasauki wani kuma yazo da tsauri addua itace magani kiyita tsayuwar dare kina kaiwa Allah kukanki akan yazaba miki mafi alkhairi muma kuma zamu tayaki da addua amma kisani duk abunda kika ga Allah. Yayi toshine dae2 mafi alkhairi agareki, gara kisakawa zuciyar ki salama tin yanxu, kikoyi yanda ake danne so ayi biyayya ga u waye, joda tace hmm Allah shigemana gaba ameen

Tin randa hafsa tamata wadann maganganun seta kara Jin kamar zata rasa abdallah ah yan kwanakin nan, shikanshi abdallah yana yawan Jin faduwar gaba a duk lokacin daya tuna joda , yaukam yashirya fadamata komai, zaune suke a garden kowannensu yayi shiru da abunda yake sakawa aranshi, abdallah yafara dacewa  joda bansan meke faruwa ba se intajin faduwar gaba aduk lokacin dana tunaki, joda tace nikuma jinake kamar sanadin rabuwarmu natare damu, abdallah yace kamarya kenan

Joda tace abdallah ji nake ajikina yan kwanaki kalilan suka rage mana murabu da Juna, abdallah yace hava joda yakike irin wann zancen ay seki saka narasa dayan side din jikina, domin ke rabin jikina ce , joda kam fashewa tayi da kuka, abdallah yakaraso kusanta yadan janyota ajikinshi yana lallashinta ana haka Sega gwaggo tazo wucewa tsananin bacin rai taji lokacin data hangesu rungeme da Juna , jodaaaaa takirata da murya mai karfi, dasauri joda tadago tareda janye jikinta abdallah kuwa zare ido yayi, gwaggo tace wlh baxan taba yafe maka ba idan ka lalatamun "ya , abdallah yace Dan Allah gwaggo kidena mun kallon ma yaudari wlh son tsakani da Allah ne

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�0鈨�
Gwaggo tajuya afusace danko zuciyarta takawo baxata jure tsayuwa ba , joda tamike aguje zata bita abdallah yarike mata hannu joda ta girgiza masa kae , abdallah yace karki bata hakuri yanxu ki bari harta huce joda tace koma yane yanxun kasakeni hankalina at ashe yake inajin tsoro, abdallah yace shikenan ,tana wucewa yadafe kanshi omg ya Allah kamun gata a wann lamarin

Gwaggo kam share joda tayi gabaki daya tadena shiga lamarin ta, joda tin tana hakuri har tafara kuka da rashin cin abinci, hafsa talura da halin da halin datake ciki, tayi2 da ita taki gaya mata komai, dole tasamu gwaggo itama din cewa tayi kibarni da ita hafsa dole badan tasoma tafidda kanta a lamarin, daga lokacin tafara tsoron tsayuwa da abdallah shima haka dukda cewa kuwa tana missing

dinshi sosae da sasae, yau sundawo islamiyya itada hafsa tafe suke suna firar bikinsu joda tace nidae hafsa inajin tsoron xua bikinku kinsan yanda yayanki yatsaneni hakama su hjy barema amaryar inkinga yanda take hantarana ma basauki , hafsa tace hava joda bruhh batsanarki yayi ba rayuwar shi hakanan kowa yana iya yiwa hakan Dan Allah kiyi hakuri kicirewa ranki hakan, bashida sabo ne barema nacemiki idan kun saba zai bari, joda tace hmm bakisan wasu abubuwan dasuka faru ba bayan tafiyarki, acikin ranta take wann zancen

ganin abdallah yasaka ta manta duk wani bacin rai, dasauri ta isa gareshi , ya abdallah shine kagujeni koh " abdallah yace joda bana son naja miki matsala ne tsakaninki da mahaifiyarki, hafsa ta karaso tace zanshiga ciki kisameni, joda tace toh ganinan xua fiarar su suke gwanin sha'awa kowannensu yana nunawa Juna irin son da yake yiwa Dan uwansa, joda tabuka sgegiyar kara sakamakon bulala dataji a bayan ta haka adinga zuba mata dorina,

abdallah yaturata da karfi mamma kashe ta zakiyi ne kome? Hjy tace abdallah wlh zan kashe ta matukar bata rabu dakai ba, abdallah yace niyakamata ki kashe ba itaba domin ni nake biyar ta ba itaba, hjy tayi tsalle tasake bugawa joda dorina joda tazube kasa, hafsa tafito aguje tareda sauran masu aykin gidan , gwaggo tafito tayi tsaye tana kallon su, abdallah yace wlh hjy idan kika jimata ciyo agidan nan  kowa bazaiji dadi ba wlh zan to tonawa kowa  asiri sekuma yafashe da kuka jikin hajiya yayi sanyi gwaggo kanta ya bata tausayi

A yanda taso zata karawa joda wani dukan amma kuma ganin yanda abdallah yake kuka da sanbatu yasaka jikinta sanyi, joda takara fashewa da kuka saka makon jinin data gani akafarta hjy tayi fuuu tawuce tareda yada dorinar hafsa tazo dasauri tajanyota abdallah kuwa yabisu har daki yana dada basu hakuri, a hanyar garden ya hadu da gwaggo dasauri yaduka yana bata hakuri tareda zayyane mata yanda sukayi da dad dinshi, yakara dacewa zan dena kula joda har se randa aka mana baiko,

Gwaggo tace tashi bakomai Allah zaba mana mafi alkhairi ameen " Joda kam kuka take kamar me badan komai ba sedan in ta tuna kiyayyar da hjy ke mata, dakyar aka samu tayi shiru, abdallah kuwa doctor yadauko yadubata aka mata dress din gurin, kulawa yake bata kamar me abu kadan zaice me, me kikeso, hafsa kanta tana tausayin yayanta yanda duk yawani canzawa lokaci guda yazama silent fiyeda tunaninka

Bayan kwana uku tawarware har takoma islamiyya , iyakacin su gaisawa da abdallah joda najin tsoron tasake cin wani dukan , abdallah kuwa bayaso yasake jamata wani abin , gamida gwaggo kuma bayaso tasake kamasa da wani laifin baya da abin Kare kansa , joda takira doctor dinta tace wai nikam se yaushe zamuje gurin matarka ne " dariya yayi sann yace kefa kin cika azarbabi , ba nagaya miki cewa dakaina xanxo muje tare ba, idan nasamu chance. joda tabata fuska tamkar tana ganinsa nidai idan aka wuce wann tym din banaso I mean cikin wann satin...........

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�1鈨�
Yau Saturday yaune Ahmed zai dawo, kuma yaune za'a fara biki, hafsa tazo tacewa joda Dan Allah zoki rakani mugyara dakin bruhh Ahmed, joda tace aza hannu aka, tace wah ni tufa mun asiri wlh ba inda zanje mezanyi a parlor dinku kuma har dakinshi sokike yakasheni tabb kedai Allah kiyaye hanya  , bayan da hafsa batayi ba amma firr taki xua dole taje ita kadai

Bayan tagama ne tazo ta kawowa joda kayan da zasu saka, English wear ne riga da skit sekuma Dan kwali fari riga baka skit pink, da talkami farare da baki komai iri daya, khalthum kam kamar tasan abunda zasu saka itama tasaka nata amma ita shigar marron colour da milk bakaramun kyau tayi ba , hakama joda yaran kamar "yayan turawa khalthum ce tanada musu dankwalin kamar head.

A motar hafsa sukaje basu bari angansu ba "nice day" ce saboda haka kowa irin shigar yayi barinma amarya abun basauki, hotel suka dauka babba a nata ciye ciye ga lemuka kamar ruwan panpo, duk inda sukayi idanun jama'a na kansu, musamman joda ana son sanin ko yar waye yanda suke kama da hafsa dakuma Ahmed, mansura tadauki loudspeaker tafara godiya ga kawayenta yan uwa da abokan arziki sann takara da yan gayyar sodi, khalthum tace kaddai dani take billahillazi bana daukar kaniya ba shegiyar data isa , hafsa tace clm dwn mana khalthum bada ke take ba mutun nawa yake gurin nan taya zaki gane hakan

Khalthum tace to meyasa taje an mata pics da kowa banda mu, nida joda idan bamuda alaqa da ita kefa, hafsa tace duk ba wann ba yanxu tashi muje kugaisa, khalthum tace banda kyau fa wlh idan tamun rubbish ramawa zanyi, hafsa a'a khalthum Dan Allah kiyi hakuri abun a kaina zai dawo bruhh yaci kaniyata  , khalthum tace shikenan muje, joda kam jinsu kawai take haka suka jera su uku anata kallon su, gurin amaryar suka nufa ankunna wakar JustinB suna Dan taka rawa, hafsa tace anty ga kawata seda ta maimaita sann tace toh ya akayi, hafsa tace wae nace ku gaisa ba, mansura tace ok ina jinta, khalthum seda takalleta sama da kasa sann tayar, tajuya abunta,

joda tace ina.....bata karasa ba tace Dan ubanki bance miki ko kallona kada ki kara ba shegiyar yarinya kamar mayya sewani barawon kyau take kamar aljana, hafsa taja hannunta suka koma mazaunin su haka bikin yakasance se hantarar su ake barin amina ma dataki yiwa kodayansu mgn , suna zaune Sega Mahmud shida wasu kawayensa, sun zo kawo flowers da chocolates, Mahmud tin daya ga joda yake kallonta dakyar yabar hall din yakirata taxo , khalthum tashiga tsokanar ta yarinya mai maxa biyu abdallah da Mahmud nikuma asea nace harda Ahmed 馃槼馃樂

Hafsa gabanta yayi muguwar faduwa dasauri takauda kanta lokaci daya taji gurin ya gundureta , khalthum tace lfy hafsa, hafsa tace bakomai kaina yake ciyo inaga zankoma gida, khalthum tace ayko se muwuce nima naqagu da gurin nan, amota suka same Mahmud da joda ,dasauri hafsa takauda kanta daga dubansu, harzata tada mota, Mahmud yace akulamun da joda nah fah karki bi hanyar duwarwatsu,

Hafsa tayi murmushi taja motar dakarfi, segidansu khalthum duk firar dasuke bata jinsu , suna isa gidan  hafsa tafito tareda banko ganbun dakin dakarfi, joda tamaza tafito tariketa tace hafsa na lfy waya bata miki rai, hafsa tace bakowa joda kaina yake ciyo ina son nakwanta, joda tace ok toh muje narakaki hannunta tarika suka shiga parlor anan tahadu da hjy dakuma abdallah ko kallanshi batayi ba, abdallah yace lfy naga kinrikota haka joda tace batada lfy kanta yake ciyo, abdallah yace ayya Allah yabata lfy " jekikaita kizo kikarbi magani abata,

Bayan takaita daki tafito tasamesa shikadai yabata magani yace tabata takoma tabata magani tasha tamata Allah yakara sauki sann tafito dae2 step tahadu da abdallah yakuramata ido itama haka, haka suka dinga karaso wa har takai suna Jin nunfashin Juna, bakinsa yakai anata tuni talumshe ido da niyyar karbar sakon kiss dinshi , lebensa ya aza anata "

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�2鈨�
Abdallahhhhhhhhhhhh sukaji ankirata dawani irin lion voice  dika gidan seda yadauka dasauri suka janye tareda juyawa domin sanin waye 

Ahmed yasha bala'in toka fuskarshi ba annuri , yace abdallah kakiyaye kanka gataba matata nayimaka lamuni har nagaji kaki fahimtar hakan Sam baxan jure ganin kana tabamun mata ba, abdallah yace Ahmed yaushe kafara shaye2 joda dince matarka yarinyar daka tsana bakaso ganinta, Ahmed yace komadae yane baka bukatar bayani daga yau nayanke duk wata alaka atsakanin ku

Abdallah yace wlh baka isaba bruhh idan bana maka musu yau zanfara, dae2 nan hjy tafito itada dad meena ma tafito tareda mansura Jin hayaniya tayi yawa, joda kam ta tsorata, dad yace meke faruwa Ahmed? Ahmed yace dad kaga yawa abdallah yafita harkar matata nagaji da wann wasar "yayan karan , dad yace kowa yaxauna , mansura tace wae matakarka honey koday kasha abun ne " Ahmed yace zanci ubanki wlh ubanwa yake shaye2

Dad yace ku min shiru hafsa tafito rike dakai tazauna kusaga Ahmed tamika masa eviron drink  , ya balla mata harara, ta girgiza masa kai hawaye na fita a idonta, shikuma abunda yatsana kenan kukan ta dole yakarba ya shanye atake yaji relief " dad yanna bell din gidan Sega kowa da kowa, hjy tace wae lfy ake tara mana bayinmu anan, dad yace karki sake mgn kinji nagaya miki

Bayan kowa ya hallara harda su gwaggo, dad yayi gyaran murya yace toh ranar wanka dae ba'a boyon cibi, a lokacin da za'a auren joda da yasir, suka watsa mana kasa a ido suka wulankantani agaban abokai na a ranar nadaurawa joda aure da Ahmed tareda amincewar mahaifiyarta , Ahmed yafirgita kwarai lokacin dayaji hukunci na batareda neman yardashi ba, amma dana bashi mgn nida yayana seya dauka ya kuma hakura

Mansura tace billahillazi bazai taba yuwaba mijina shine mijin wann tanuna joda, wadda ita Sam bata san yaren da suke ba , hjy tace yasaketa kawai aydama kunya kake gudu kuma yanxu komai yawuce, Ahmed yace bawanda ya isa yasaka nasaketa , joda kanwata ce jinina ce da uwarta da tawa uwa dae uba dae! Gwaggo tace yaushe muka hada jini dakai ? Ahmed yace tin randa nafidda joda aruwa nake tunanin akwai wani abu a tsakaninmu domin yanda nakejin hafsa haka nakejin ta

Daga ranar nake bibiyar asalinku har nagane kece hafsatu kanwar mahaifiyata saratu asalin masina tashin nija, gwaggo tace koshi yasa nakejin hafsa sosae ashe munada alaka, Ahmed yace ni nayi tsaye aka kara muku kudin barin gari dayake ma lokacin bansan waye kuba inadai cikin bincike, kudinku suna account koyaushe kuka bukata za'a baku, mansura tace kai bamasan iskancin banza anjiya uwarku daya ubanku daya wlh matukar baka saki wann jahilar ba baxan aureka ba, Ahmed yatabe baki it's up to you "

Abdallah yadora hannu akanshi yana maimaita innalillahi wa'inna ilai'hir raji'un, mike wa yayi atsaye yana shikenan narasa joda narasa raina da farin ciki na, timm Kakeji yafadi kasa somamme joda tabuga wata sgegiyar kara seda kowa yafirgita domin kuwa sunma aza iska ne da ita, da gudu tadunfaro gurin abdallah tana karka tafi kabarni abdallah na rayuwa ta bazata in ganta ba idan bakai, Ahmed yacabketa tafada kanshi, bude idon dazatayi taganta ajikin Ahmed luuuu tayi itama ta some akasa............

( zanbada hakuri akan 2dyz kunjini shiru muna ta hidimar biki ne kunsan sa'a nin bikin mata so plss amun afuwa dalilin dayasa kenan nayi page 4 sbd baxan yi gobe ba se jibi  )

Abu nabiyu shine :- akwai wani  dayake juya mun novel yacanza shi daga yanda nayi nd kuma yasaka sunanshi, ni nakirkira labarina dakaina , so plss idan bakada basirar yin naka badole bane  ka yi satar nawani ba, baxakace dole se kayi abunda bakada shi ba,  seka duba idan Allah baibaka wann baiwar ba to yabaka wata kowane Dan Adam yanada tashi baiwar sedai rashin maida hankali yakansa mutum baisain baiwar da Allah yamasa ba  { a gaskiya baxan yafewa duk wani mai juyamun novel ba

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
   馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
       馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
         馃巹 馃巹 馃巹
            馃巹 馃巹
               馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�3鈨�
Dad yayi gurin abdallah dasauri yana jijjigashi, hjy tace billahil'azim idan dana ya mutu senayi kararku akotu Sam baxan ragawa kowa ba, kuma wlh kigaggauta karye asirin da kikayi wa dana Dan banga abunda yake cikin yarki  ba da har zata saka shi ciyo, gwaggo tace nagadai ba danki kadai ne yashiga tension ba harda tawa yar,  amina tace dallah yimun shiru, Ahmed yace kee zan tattakaki wlh, da ke ake mgn , mansura tace nidae ba wann ba wlh kawai kasaketa,

tsaki yabuga mata ya cakumi joda aka fadarshi se dakinshi hafsa tarufa masa baya , dad kuwa yakira family doctor dinsu domin yaduba abdallah hjy tabarsa dashi sekuma amina data tsaya domin tana Jin tausayin yayan nata, mansura ma tabi hjy, hannu ta aza akaii na shiga uku anty yanxu yazanyi da son Ahmed wlh bazan jure ganin wata a matsayin matarshi ba, hjy tace ke kinutsu,

ni wlh dadi naji anraba dana da kaya, yarinyar batada wayo ga shegen tsoro, kawai yanda zakiyi kimaidata boyarki itama dole as an abunda aka kulla mata shikanshi Ahmed din bafa sonta yakeba, kawai sbd tana yar uwarshi ce, kokin manta yanda yake wulakantata, kedai kawai yar ayki kika samu kinfita waye wa dakomai se yanda kikayi da ita, kinga wann abun tawarware mana hanyar rabasu da abdallah, ga abu yajo mana asauki

Mansura tace hakane anty kwakwal warki naja wlh, se yanxu naji hankali na yakwanta da kuwa har jinina yahau, to yanxu ya zancen abdallah, hjy tayi murmushi har nake yanke masa shawara sati mai xua yabar Nigeria kawai myb acan yasamu relief bafa karamin so yake yiwa yarinyar nan ba , mansura tace bari anty wlh yabani tausayi yanda yake kuka

matsalar yarinyar ce kyakkawa gata da shiga rai komai nata abin birge wa ne koke mace zaki so ace yarki ce bare kuma namiji, hjy tace sosae yanxun dae karki yarda ta waye agidanki duk abunda zai kawo mata cigaba karki yarda dashi Hjy tace yanxun kije kibashi hakuri kice bakomai zaki riketa amatsayin kanwarki kinjanye zancen sakinta adaura

aurenku kawai, Mansura se antyna "fitilar Sheri ko babu mai kina kai safe" hjy tayi dariya kedai jeki tuggu xamu hada mata da kanta seta gudu agidan , mansura ta daga hannu a gaida sarkin mugaye, dakin Ahmed yace tanufa , shiga tayi kawai batareda sallama ko neman izini ba, hafsa da Ahmed suna kokarin sake mata wasu kayan sakamakon zazzabin datake amai kawai take batama san waye kanta ba,

Ahmed yadago yace kinbiyoni danki karamun wani rashin kunyar koya Mansura tace a'a dear hakuri naxo baka akan abunda namaka agaban siblings dinka, kasan kishi irin namu na mata daga baya kuma naga bakomai bane joda batada matsala indae har na riketa amatsayin kanwata, Ahmed yace wai an gaya miki ina sonta ne? Mansura tayi murmushi dukda baka santa dole kadauki kaddara da baka santa ay bazaka yi kishi taba,

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�4鈨�
Ahmed yace luk mansura bakishinta nake ba zunubin da zasu dauka ne abun duba, ciki kuwa harda ni sbd basu San da wann auren ba, mansura tace toya zancen tarewa atare zamu je, Ahmed yace fuck you wazata zauna mun a gida ay wlh seday ta tabbata anan auren dai akeso ko totayi , to taya ma zan dauki wann amatsayin matata na karamar yarinya tazo tarainani Hafsa tayi murmushi tace bari in fita bruhh,

Ahmed yace au dama zama kikayi kina saurarenmu munafuka ba tace masa komai ba tafita abunta, mansura ta karaso kusaga Ahmed tace hup komai yawuce, Ahmed yamata banza ya cigaba da gyara fuskar joda mansura tace tokadaina tabata mana, dasauri Ahmed yadauke hannunsa afuskarta, mansura tamatso tajanyo fuskarsa tana masa wani kallon Ahmed yace kee lfy miye haka

mansura kam data gama tafiya tace just once Ahmed, Ahmed yace kee wai mekike nufi, kafun yagama fada yaji bakinta anasa tana masa wani ka ruwancin, Ahmed dayagama rudewa domin kuwa kankanin abu yana saka shi fita a hayyacinsa , a hankali yafada kan gado tarufa masa baya, dakyar yasamu ta sakesa tana kokarin yin wani abu Ahmed yace plss mansura kibari muba muharram Juna bane, mansura tace au to menene yayi saura kwana uku kaday, Ahmed yace ayseki jira tym tinda naga har sokike mansura tace noo hava dae shaukin so ne kawai

Dae2 nan joda tafarka da kuka ta farka abunda tafara fada shine, abdallah! Abdallah nah! Kana ina lalube tashiga yi tsavar kukan dataci har bata iya bude idonta, carab ta cabko hannun Ahmed dasauri tarungumesa abdallah wai mafarki nake ko gaskiya ni nakasa gane yaren dasuke, abdallah karka bari ahadani da yayan hafsa  , bana sonsa natsanesa kamar yanda baya sona yatsaneni, abdallah mugu du adaura mana aure , yayan hafsa wulankantani  zaiyi Sam baisan darajar Dan Adam bazanso ace shine uban yayana ba

Tass Kakeji Ahmed yawanke ta damari, mansura dake kallonsu tayi murmushin Jin dadi, ubanwa ne baisan darajar Dan Adam ba, angaya miki ko mata sun Kare aduniya zan soki bare harna hada zuri'a ta dake kazama kucakar banza jahilar yarinya kawai, joda tace wlh banice jahila ba inada ilimi, Ahmed yayi ball da ita ta saiwa ina mgn kina mgn bell yazare zai fara dukanta dasauri mansura tazo ta tare hava dae dear yazaka biyewa wann yarinyar kasanfa akwai kuruciya acikinta,

joda ta balla mata harara, ta cigaba da kukanta Ahmed yace mansura bani drink a fridge. mansura tace ok dear soya milk tadakko masa, Ahmed no ba ita energy drink nakeso, seta sake dauko masa rabena drink, tsaki yayi yakarba yasha sann yace tafita yana son hutawa , mansura tace hava baby na wai meyasa kake illegal ne seka korani, Ahmed yace to ay seki tsaya inyaso  semu shiga wankan atare,

joda najinsu se kuka take, mansura tace hmm ok zan fita wann jikin da ake boyo yakusa xua hannu, Ahmed yabuga tsaki aranshi kuwa yace mara kunyar banza, mansura tabude  kofa zata fita joda tabita zata fita Ahmed yadaka mata tsawa ubanwa yabaki izinin fita, mansura tawaigo hava dear karika mata a hankali mana yarinya ce joda kam batasan randa tafadi ba yanda yabuga mata tsawa, mansura tafita cike da Jin dadin data kasa sanin iyakarshi, direct dakin hjy taje, tana bata lbrn yanda taga Ahmed nayiwa joda hjy tace za'a rina Ahmed da kyankyamin yan kauye,

dama dae zumuncin da yace ne yasaka ya yarda da auren su kinsan fah baya wasa da jininsa duk yanda yake dinn yana da son jininsa , sekinga yanda ya yiwa wani ranar daya mari amina kadan yakaishi kotu, mansura tace tohhh ashe kam idan nayiwa joda mugunta zai rama mata tinda ita jininsa ce ,

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�4鈨�
hjy tace kamm wai bakiga yanda yake tsanar tabane mansura tace nagani mana  Ahmed  yashiga wanka yabar joda akasa tana darzar kuka, net yasaki agadonsa sann yashirya bayan ya fito yace keee zonan, joda taki xua tana dinga kankame jikinta , Ahmed yace zaki zo kose na ballaki, joda ta dinga matsowa kadan2 tana rawar jiki

Ahmed ya kamo kunnenta  idan nakara jin kinkira sunan abdallah kowani da sunan Wanda kike so sena fasa bakinki kar in kara Jin wani iskancin koke bakisan darajar aure ba joda kam takara fashewa da kuka, Dan Allah yayan hafsa tinda baka sona nima kuma bana son ka Dan Allah kasakeni na aure abdallah shikadai ne farin ciki na

Ahmed yace anki asakeki yar iskar yarinya inkika kara mun irin wann zancen wlh sena fasa bakinki ,anan zaki tabbata da aure a kanki keba gidan miji ba keba gidan ubanki ba, joda takara fashewa da kuka Ahmed yace kefitar mun adaki kafun in kakkaryaki joda ta dinga bin Gina har tafita a dakin, dakyar takai dakinsu tafadi a kasa tana kuka , gwaggo tazo tadagota joda tafixge hannunta tana cigaba da kuka , tace gwaggo ashe bakya sona kinfi son farin cikin wasu akan nawa kika badani ga Wanda baisan darajar Dan Adam ba baya sona hasalima kyamata yakeyi ya maidani kashi

Gwaggo kokin san duk sanda nayi ciyo tasana dinsa abun kefaruwa, shine voice dinshi yake sumaddani shine, shine yakarya ni da gangan yataka mun kafa shine shine sekuma tafashe da kuka, gwaggo tarungumeta tana shafa bayanta kiyi hakuri yata ina sonki fiyeda komai nawa insha Allah bazakiyi dana sani ba , joda tace na yaushe kuma har abada baxan daina dana sanin auren yayan hafsa ba, gwaggo kema kinsan bamu dace da Juna ba girman kai dagawa daukar mutane bakowa duk halinshine

Gwaggo tace bakomai zai canza, indae har kin iya shi  namiji kamar yaro ne se yanda kikayi dashi , joda tace gwaggo kina karawa zuciyata zafi ay se kana son mutum zai yadda kamasa haka ni bana sonsa shi baya sona yatsaneni 2 sekuma tafashe da kuka, gwaggo takara janyota tana lallashinta

Kuyi sorry muna biki bazan samu damar ida wann page dinma, dakyar nayi

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
   馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
      馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
          馃巹 馃巹 馃巹
             馃巹 馃巹
                馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�5鈨�
Tin randa abun ya faru joda tazama kamar wata tababbiya , hakama abdallah an rasa gane kanshi dole dad ya yanke shawarar dazaran angama bikin Ahmed zai tura shi Malaysia kozai samu relief. khalthum kanta tagirgixa dajin wann zancen  hafsa kuwa tana maijin dadin kasancewa yar uwar joda koba komai yanxu tagane dalilin dayasa bata iya barin joda acikin wani hali itama haka, wani gefe na zuciyarta kuwa yace shikenan Mahmud yakusa xua agareki , murmushi tayi Allah ka mallaka mun yah Mahmud amatsayin mijina ameen

 Yaude itace ranar daurin auren mansura da Ahmed, kofar gidan dad, cike take da Dan mutum dangin mansura danasa sekuma abokan arziki gakuma yan semun gani a gefe akwai yan kwadayi dasuka zo dan su samu garar biki, ciki harda su oo da oo , Alhmdllh angama daurin aure lfy anguce gurin cin abunci babba hotel ne dad yadauka domin mutanensa hakama Ahmed danasa daban, tsayawa fadar irin dukiyar da aka batar bata lokaci ne ku kissima aranku,

Karfe 3 aka shirya domin xua gurin walima, joda nakwance dakinta har yanxu takasa sakuwa , hafsa da khalthum sun zo suka ce tazo su shirya amma seta fashe musu da kuka , khalthum tace iyye wato kina kishin mijinki koh? Joda taballah mata harara Allah sauwake nayi kishin namiji irin yayan hafsa, hafsa tace tome aybunshi, joda cikin muryar kuka tace dallah ku matsa kubani guri kafun muyi masifa , hafsa tace muje khalthum yau tafullo ta motsa zuciya ba kar tamana sanda 馃槀

Khalthum kuwa ta dinga dariya hakane fah kin san FULANI da zuciya kamar zauna, joda tace billahil'azim idan baku bar mana dakinmu ba ....sekuma tasaka kuka, hafsa tace ohhh my joda clm down mana kisakawa zuciyarki salama, rayuwa komai seda hakuri , bakomai muke nema musamu ba watakila akwai alkhairi acikin auren

Haka suka gama zancen su joda ko motsa wa batayi ba bare nasaka ran zata tashi , dole su biyu suka shirya sukaje gurin walima ba jimawa amarya tafito shikin wata shiga ta alfarma se kyalli take wuyanta tasha zinari da awarwaro, hjy tamata iso zuwa gurin decoration din daka tanadarwa amarya ,mansura ta duba ba joda tashiga Kiran hafsa, hafsa tazo tace ina uwargidana hafsa tayi murmushi anty tana ciki sekuka take har yanxu taki sakuwa, mansura tace ollrt jeki kawai

Malama uku sukayi walima amarya kam batajin su domin ana walima tana soyewa da Dan jeneral , dayake akwai net ba'a ganin ta dakyau se itace take ganin mutane , anraba kayan walima a bun badama anci ansha an watse sekuma dinner wadda abokan ango suka tanadar  , Karfe takwas akafara xua dinner din joda tafito zata gate kamar daga sama taji muryar abdallah yana cewa zaije dinner, abun yabata mamaki wai har yasaki, aranta tace aikuwa nima se naje nagan ko zai kula wata budurwa ne

Joda nah ango cikin wani red nd white din led tasha head karami Wanda khalthum tana da mata purse dinta red takalmin ma red ne, haka hafsa da khalthum sunyi masifar kyau khalthum ce kejansu joda na baya hafsa naga ba tareda khalthum

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�6鈨�
Katon guri ne Wanda yaji decoration gurin amarya da ango basauki lemu ka gasunan da kaji nama ko wanne iri kakeso, kowane grp din kujeru da kafar rago agurin gakuma pizza da cheese se abunda ranka yaso nikaina yawuna seda ya tsinke kadan nace a sammun ,  su joda sun shigo sun yiwa kansu guri itada su khalthum da hafsa, bayan minti biyar Sega ango yashigo rikeda amaryar sa sunyi shigar fararen kaya weeding gown ce tasaka da net a kanta bakaramun kyau mansura tayi ba bare kuma angon daya hade cikin mayyar shadda da hula baka bantaba ganin Ahmed cikin manyan kaya ba, khalthum tace woww joda dubi mijinki

Joda tabuga tsaki wlh banaso khalthum wlh zamu saba dake waye mijina ay dae agama biki ni wlh seya sake ni nakasa In auri wanda nakeso , ana haka Sega abdallah, tamike dasauri ta taresa, cak yatsaya yana kallanta dae2 nan aka fara kidi light tafada kansu tinda atsakiyar guri suke , dasauri tajuya zata koma ma kidan yafara kanwar ango da kanin ango subuda fili da rawa , joda taware ido abdallah kuwa yajuya mata baya kidi akasa joda kam tashiga rawar jiki se juye2 take ana haka Sega wata yar kwalisa tazo tana zuba musu kudi dole abdallah yajuyo yafara takawa joda kam tsaye kawai take takasa motsi

Hafsa taji tausayin ta tazo tajanyota zuwa kujerun dasuke zaune khalthum kuwa mezatayi inba dariya, at kinga masoyinki koh? Joda tafashe da kuka se hafsa ke lallashinta, duk abunda ake visa idon Ahmed da Mahmud Wanda yagama kuluwa , mansura kuwa se murmushi take na mugunta, haka taron yakasance Ahmed yazuba dala kamar ruwa haka yake barin kudi agurin Mahmud ma ba baya ba,

Hafsa tace kuzo muyi wa amarya da ango liki, joda tace wah ay wlh dana zuba musu kudi na gwara na zubasu a shadda, khalthum tace kyaleta hafsa kishi take ,joda tace tupp Allah sauwake inyi kishin wancan mai mugun halin , hafsa tace nidai yayana bayada mugun hali kema Dan kinki kwantar da hankalinki ne " joda tace nace dai bazaniba sekun dawo dole suka kyaleta sukaje suna yimusu liki,

Wucewarsu keda wuya Sega wani yazo yaxauna baby tin dazu nake neman tayadda zan sameki mugaisa , joda tadago tace lfy? Yace lfyr ce dai wlh kawai kimun kuma ina sonki in bazaki damuba muje filin rawa, joda tace amma wlh kai bakada kunya nizaka cewa muje filin rawa namaka kama da mai rawa ne iye , Mahmud yaxo wucewa yagansu dasauri yadawo baya, yace kai malam lfy? Yaron yace lfy qlw bros dama naganta ina sone, Mahmud yace itakuma bata gayamaka cewa ansaka muna rana ba, joda tadago tana kallonshi yace to maxa kabar nan gurin wann matata ce, yaron yabashi hakuri sann yawuce

Mahmud yaja hannun ta yace zo muje gurin rawa joda tace a'a ya Mahmud ni ban iya rawa ba , Mahmud yace sekuma kinje dole, haka sukaje yasakata dole tayiwa amarya da ango liki, Ahmed se bin ta da harara yake mansura na mamakin yanda yarinyar tahadu amma Sam bata gaban Ahmed duk yan matan gurin babu wacca tafita yayan masu kudin gurin da kowa , dayake khalthum ce ta gyara ta, khalthum akwai duniya ci dason wanka

Mahmud yace kiyi rawa mana se in miki liki , joda tace kunya nakeji ya Mahmud bantaba rawa ba ni banma iya irin wann ba, Mahmud yace shikenan toki Dan taka, haka kuwa akayi yafara mata liki, abdallah na hango su nashi kishin ya motsa shima yaxo yana mata likin kudi, aykuwa se abun yazama kishi dollars, aykuwa mai kidi yakoma kansu yana xuba kirari joda kuwa duk ta tsargu

Hankalin kowa yadawo kansu, Ahmed yarungume hannuwa yana kallonsu khalthum da hafsa sukayi jugum suna kallo, sukuwa sunki daina mata liki duk da barawa take ba, hafsa taje gurin mai kidi tace yasaka musu kidin FULANI, aykuwa Sega joda tafara motsawa duk Wanda yake FULANI agurin seda yaje filin rawar saboda yanda suke Jin kidan ajikin su...........

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�7鈨�
Joda tafara wani irin rawa yanda kidin ke tafiya haka rawar ta ke tafiya kowa yakoma kallonta hafsa takalli khalthum ashe ta iya rawa jita kamar macijiya, kowa yamatsa yabata guri Mahmud ya cigaba da liki hakama abdallah, gumi se karyemata yake amma taki bari shikuma mai kidi yakara da busar FULANI, nan joda tafara ajujuwa har takai gurin Ahmed anan tafada kanshi tareda rungumesa da hannu bibbiyu, hafsa tace yayi dae2 khalthum tace yo naga soyy,

sun dade ahaka sann Ahmed yadago fuskar ta yaga idonta arufe Jan ta yayi yanda take rungume ajikinsa har mota, abdallah ya dinga ja dabaya yana dana sanin abunda yayi, mansura tabiyosa dear ina zaka ay seka bari hafsa ta maidata gida, Ahmed yace noo kikoma ina xua, gudun yamata wulankanci cikin kawayenta yasaka takoma, Mahmud yaxo yace man......baikarasa ba Ahmed yasaka hannu agabanshi batareda yajuyo ba yace enough enough Mahmud,

yana kai nan yasa kai yawuce cikin motarshi ya ajiyeta yazagaya yatada motar se gida haka ya rungume ta tamkar jaririya, se dakinshi ya shimfideta kan gado sann yadauko mata ruwan sanyi yabata tasha tareda wani kyalle yagoge mata fuskarta, ar u ok? Naji yafada joda ta girgiza masa kai, sekuma tasamasa kuka, Ahmed kam shiru yayi yana kallonta can yace kinsan Allah Zane ki zanyi

Yanxun Dan bakida mutunci kikaje karti suka tasaki a tsakiya suna tabaki wann yatava boobs wann yataba hibs , kowa na kallonku, joda tace na shiga uku ni wlh bawanda yatabani acikinsu, Ahmed yace yimun shiru munafuka dama ay haka kikeso , ke baki San hukuncin aure ba koh " joda tace toni ay bana son auren ,Ahmed yadaka mata tsawa zanci ubanki wayake son auren daga an taimaka miki akayi, joda tace toni nagode da taimakon, Ahmed yace keee wlh zakici ubanki yanxu get out b4 nabata miki rai shegiya mai fuskar agwagwa ," nikuma asea nace ay fuskarku daya ehe 馃槒

Fita tayi takoma dakinsu, gwaggo tace au har kun dawo inasu khalthum da hafsa, joda tace basu dawoba, seni kadai, gwaggo tace ke kuma ana zaune qlw sekika yanke jiki kika dawo gida, joda tace toni nadawo ne ay yayan hafsa ne ya maidani gida, gwaggo tace tsakaninku baruwana, joda tafashe da kuka ni wlh an cuceni kawai baza'a bawa mutun Wanda yakeso ba mezanyi da wann Dan bakin rai, gwaggo tace kyaji dashi in ni nacuceki toki gayawa Allah inyaso seya saka miki, joda ta zunbure baki tayi cikin dakin

Tellphone tajanyo takira doctor bayan sun gaisa, yace toh ganinan xua nadai san abunda kike jira, joda tayi murmushi yauwa likita kagane, bara nayi sallah kafun kaxo , sallah tayi sann tasake wanka sabuwar atanpa tasaka ta cikin kayan bikin super ce tamata kyau sosae sann tasaka gyale kalar atanpar se takalmi flate, gwaggo sallah take saboda haka ta lallaba tawuce batareda taganta ba , tana kai gate yana fakawa da mota kawai tashige, suka tada hanya , wakar flavour yasaka mata mai taken vewrifull" joda najin dadin wakar sedan mamin take dikda bata iyaba , har suka kai wani gida mai kyau, yakalleta yanaga jikinki yafara bari zakiga queen of beauty " joda tace uhm..Muje dai , shi yabude gate din abunda yabawa joda mamaki kenan sann suka shiga

Karamun gida ne amma yahadu komai naciki sabo ne " binsa kawai take itakam bataga alamun wani mutum agidan ba, joda tace nikam bakowa ne agidan, yace bana son azarbabi fah muje dae, wani daki suka shiga se kamshin sababbin kaya yake , yace tazauna yakira mata matar tasa joda tazauna cike da kaguwa, ba'a Fi minti uku ba se gashi yadawo da drink yana sha yace dubo nan joda ya nuna mata mirror wakika gani, yarinyar nan tafiki kyau luk at pinky lips dinta bakinta kamar cokalin tea gashin ta har gadon baya komai nata enough ina kewar ganinta nanda shekara daya , joda tajuya tarufe idonta, da hannuwanta, likita yace hakika joda so yawuce afadesa da fatar baki ina sonki joda tin randa nafara ganin ki, joda kam kasa tsayuwa tayi aranta tace shikuma wann nasa style din daban yake..........

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
   馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
      馃巹 馃巹 馃巹 馃巹
          馃巹 馃巹 馃巹
             馃巹 馃巹
                 馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�7鈨�
Haka suka dawo gida Zancen namata yawo akai, kowannensu da abunda yake sakawa aranshi, joda na tunanin makomarta shikuma yana tunanin karta ki karban soyyr shi, joda tace nikam likita se yaushe zanga fuskar ka? Dasauri yataka burki seda ta tsorata, yace no joda bayanxu ba lokaci baiyi ba , joda tace towae mekake boyewa ne acikin wann fuskar, yace bakomai joda mamaki ne kawai aciki dakuma tsoro,

Joda tace tsoro kuma kamar ya? Yace eh tsoro nasan idan kika gan fuskar nan komai ma zai iya faruwa idan ki kaga hallitar da Allah yamun wann dalilin ne yasaka nake saka face mark nafi son kiso zuciya ta sama da fuskar nan tawa ganinta bayada wani amfani Watakila ma idan kika ganta bazaki sake yarda ko hanya ta hada mu ba, joda , kam dole ta hakura ,

yana ajiyeta Sega su hafsa dasauri joda tashige gida batareda sun ganta ba, tayi shiru kamar mai bacci, koda su kazo tana bacci khalthum tasha dariya sann suka fita, wanka tayi sann tasake wasu kaya , tana cikin shiri segasu sundawo , hafsa tace muje gurin kae amarya, joda tace wah zaije kai amarya din. hafsa tace tome ne aciki Dan kinje, joda tace Allah sauwake mun naje kaima wani mugun amarya toni waema miye ruwana dasu nifa danke nake xua bikin nan hafsa

Hafsa tace ollrt yanxun ma kije danni okey, joda tace wlh ba inda zanje kubace mun dagani, khalthum tace muje hafsa kar mu rasa motar hawa mudae baza'a bamu lbr ba, joda tace safe journey. khalthum tace oho dai kedai kishi ne kurum bazaki iya ganin mijinki dawa ta ba amatsayin matarshi, joda taadauko filo ta jefa mata sann tafashe da kuka dasauri suka bar dakin

Gwaggo tace to lfy sarkin kuka, joda tace ni wlh ki musu mgn sudena tsokanata wae daga nace bana xua shine wae ina kishin yayan hafsa ne " gwaggo tace yo dama meke cinki inba kishi ba, joda takara fashewa da kuka tana bubbuga kafa , ko Dan kwali bata saka ba tafito waje tayi hanyar garden tana kuka, bayan wani window ta tsaya tana kuka tana zance ita kadai, kamshin tirare taji dasauri tadago taga waye fararen kafafun sa ta zubawa ido sann tayi sama light din wurin yaki kae ga fuskarsa amma dae tasan abdallah ne sbd shiyake saka irin wann kayan

Dagudu taje tayi hugging dinshi tana kuka, ya abdallah shikenan kahakura dani, Dan Allah mugu du daga gidann, bana son yayan hafsa natsanesa kamar yanda yatsaneni, sekuma tasaka kuka, tareda kara kankame shi, shiru taji yayi a hankali ta sakesa, tana son ganin wani yanayi yake ciki , amma fuskar shi bama ita yake kallo ba kujera tajawo tahau yanda tsawonsu zaizo daya , na shiga uku tafada 馃檰馃徎 tareda zare ido " Ahmed yakura mata idonsa masu ban tsoro fuskar nan ba annuri acikinta , yasaceki kugudu yafada acikin lion voice dinshi? Wato ke yar iska tantiriya koh har kinsan saurayi ya daukeki kugudu domin kuji dadin aykata masha'a

Joda tace wlh a'a bahaka.....bata karasa ba yabuge mata baki sann yakwabe kujerar tafadi akasa, joda kam tini tasaka mishi kuka, Ahmed yace wlh yanxun zakici ubanki idan bakimun shiru ba shegiya munafuka , musa afuska fir'auna azuci, joda tashiga girgiza masa kai hawaye na fita a idonta, dagota yayi sama sann yace idan bakiyi hankali ba wlh boarding skull zan mai daki tinda ke ta tacciya ce. ..........

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�8鈨�
Joda tace ni wlh bazanje boarding ba haka kawai arabani da gwaggo na,  Ahmed yakwabe mata baki ina mgn kina mgn koh? Joda tasadda kae kasa tana hawaye kafarshi yasaka yayi ball da ita sann ya juya yabarta agurin kuka take kamar me, aranta kuwa cewa take Allah yasa yafusata din yasakeni , nidae nace ameen kufa 馃

Tin lokacin joda bata kara zancen abdallah ba koma ganinsa bata sake yiba sema lbr dataji cewa yatafi Malaysia  gun hafsa daga ranar tafidda shi aranta amma can kasan zuciyar ta na sonshi, hafsa ma takoma skull, su joda ansha kuka kamar me, dakyar ta hakura itama hafsa din tasha kuka ciki harda kukan rashin samun soyyr Mahmud da tayi, atunaninta kafun tadawo yayi sabuwar budurwa,

idan yafahimci joda nada aure, wata zuciyar kuma tace koday kigayamasa, can kuma tace noo bana kishi da yar uwata,  to amma kuma miye amfanin boyewa din dawann tunanin tabar gidan Gwaggo tagama fura tamikawa joda tace takai a fridge din babban palor na gidan, a hankali take tafiya har ta isa gurin tabude fridge ta jiye furar sann tajuyo, dae2 nan suka ci karo da amina nanko joda ta tsaya cike da tsoron abunda zata mata,  amina tadinga zunburo baki kamar mai shirin daukar selfie,

joda tarava gefen ta zata wuce amina ta tare hanya, sann tace sannu anty joda matar big bruhh, sekuma ta kyalkyale da dariya , joda kam tini tafara ruwan hawaye, amina tace au kuka ma zakiyi, dubeki Dan Allah wae ke kin waye koh? tobara kiji maganar da bata tashi wlh wlh wlh sau nawa? Joda cikin muryar kuka tace uku, amina tace gud to wlh kar na sake ganin kinyi kwalliya kokuma kinsa ka kayan masu kama da na yayan manya danke bayar manyan bace tsiya gaba tsiya baya

Kuma daga yau kexaki riga gyara mana dakinmu nida hjy sann kirika wanke mun under wears dina okey tareda jamata kunne, joda tace ollrt anty amina ta mata soko alright, ni zaki yiwa speak yaushe ma kika shiga skull din. kar nakara jin kinyi speak wlh sedai kiyi hausa ko kuma kiyi fulatanci ay muma munaji , joda tace insha Allah zan kiyaye, tajuya zata wuce

amina ta janyota zo muje na nuna miki toilet dina akwae pants dina uku dasuka baci da mensis dina zaki wanke kitabbatar kinsaka Gishiri kadan da dettol  akwae  warm water dasu zakiyi amfani  idan kin gama ki dauraye da hypo dauraya na biyu zaki gan tirare Wanda ake sakawa saboda karnin sabulu ko karnin blood din understand?  Joda tace yes, amina kuwa tabuge mata baki wato har kin manta

**** abunda yakamata kowacce mace tayi kenan domin Kare kanta daga cutar infection sann zaki iya insert na miski fari ko zaitun da habba domin kara tsabtace HQ dinki musamman matar aure ko budare suna yi infection base mai aure ba so kowa seta kiyaye marta barta , gyaruwar HQ dinki shine martabarki  ( Allah yasa mudace  ameen )****

馃巹 FULANIN DAJI 馃巹
N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�9鈨�
Haka joda taje ta wanke pants din xuciyarta se tashi yake sann tagyara mata dakin Tass ko ina seda tagyare tsab ta kunna tirare , tafito kenan tahadu da hjy a downstairs, hjy tabita da muguwar harara dasauri joda ta nemi sauka, hjy tayi saurin jawota inazaki munafuka,

mekikayo adakin yata, amina tace kyaleta hjy ni nasaka ta ayki, bara naduba wlh idan baimun ba sekin kara wani, dakin tashiga tana Kare masa kallo yanda yadawo Tass harda can zamata jerin daki kuma bakaramin kyau yayi ba, tafito tana kinci sa'a yarinya yanxun sora dakin hjy, joda tace lokacin sallah yayi fah,

hjy takai mata ran kwashi lokacin sallah dayake mu kafurai ne koh? Joda tace a'a bahaka nake nufi ba hjy takwabe mata baki yimun shiru makirar "ya , maxa jeki gyara mun nawa, tana shiga amina  tace wlh hjy ta iya gyaran daki dubi fah yanda dakina yadawo harda canza style aikam da baimun kyau ba senaci ubanta tinnda bansakata janzamun kaya ba,

hjy tace ohhh....kice munsamu yar gyaran daki, amina tace sosae ma hjy kinga munsamu hanyar cin ubanta , da aeki kadae semu maidata tsofuwa  wahala tamaida ita baya daga baya dole mijin yasaketa inyaga ko kallonta baya iyawa Bari kiji hjy nahana ta saka kayan kirki sann nahanata make up da wann shegen speak datake yanxu kuma bara taxo sena hanata daka bra yadda boobs dinta zasu zube awar silifa ,

sann wanka a sati sau biyu banda saka tirare, hjy ta kyalkyale da dariya kae amma dae se yau nakara tabbatar ni na haifeki wann bala'in haka yo ay kice yarinya tazama hoto duk wata hanyar gyara kin tosheta, amina tace baki wasan wann ba sena gusturemata gashin nan nata yanda natsani nagan ta zuvo shi, hjy tace nagode yata nabaki dama kiyi duk abunda yadace

Tana fitowa amina tasata agaba da scissors, tagutsire mata gashin ta yakoma kamar nawata baby, sann tabata wata sabulu tace dole da ita zaki rinka wanka kuma nagaya miki sau biyu ko uku zakiyi wanka asati daya , sann tabata baseline dinda zata shafa dakuma man kitso joda kam ba tagane kona miye ba, bacin ranta daya ashe wae bata wanka kullum amma in bancin haka babu abunda yamata zafi gashin ta kuwa dama ya isheta da

Gwaggo tasama zaune tana karanta iziya, gwaggo tace ke kuma daga kae fura sekika maida gari naku joda tace wlh a'a gwaggo anan takwashe komai tazayyane mata amma taboye zancen wanka da gutsure gashi duk taboye kawai dae tagaya mata cewa itace zata rika yimusu gyaran daki, gwaggo tace to miye aciki ay duk acikin aykinmu ne " kodan kinga sunbarmu muna cin bulus, koba komai ma kinga zaki kara kwarewa da ayki a yanda kike da shegen son jikin nan, joda kam tabe bakinta tayi tashige daki tayi alwala ta tada sallah

Su mansura kuwa se zagwadi ake an shigo gidan Ahmed, randa aka kawota bai shigo gidan ba se kusan 12 shima itace tamatsa mashi da kira danko yamanta cewa shiwae angone duk wata waya tashi daya san za'a nemeshi kashe ta yayi, yana kuwa xua ta taresa da hugging, hannunsa take kallo bataga ledar kaji ba, aykuwa tasa tanbaya Ahmed yace nasiyi miki kaji sekace wata mayyar nama kaxarma wace iri ce bakiciba , mansura tace hakane honey muje daki na, Ahmed yace to mezanyi a dakinki nifa bacci nakeji seda safe, mansura tace bazamuyi sallar godiya ga ubangiji ba, Ahmed yace kyayi ke kadae danni na rigada nayi shaf'i da wut'ri.........

Muje zuwa 馃巹
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/29/16, 12:04 AM - Queen Safiyyert馃憫: FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�0鈨�
Daga ranar joda tazama kazamar karfi da yaji tin
gwaggo bata damuwa har abun yafara cinta , a
skull ma haka khalthum kefama da ita idan
tamatsa mata seta saka mata kuka, gashi lokacin
zafi ne " haka zakiji tana ta wani tsamin ba dadi
duk yanda khalthum taso daure wa amma ina
dole ta canza site ,
Ba abunda yafi damun kh irin bakin da joda keyi
skin dinta duk ya takuje yayi wani iri dashi harma
kara gwaggo da ita, abu dayane bata bari ba
shine karatu dukda suna gab da fara paper, agida
kuwa tazama boya tana dawowa skull sometime
ko sallah batayi zakiji anzo nemanta hasana mai
ayki kuwa tayi ta masifa acewarta wahala ce
tamaida joda hakan, yau Mahmud yakawo musu
ziyara tareda chocolates dinda yasiyowa joda,
bakaramun mamaki yayi ba ganin yanda joda
tadawo kamar yar 60 , dakyar yake iya zama a
tareda ita, Mahmud yace joda ke kuwa wani irin
ciyo ne haka kinbi kin rame kinyi baki komai naki
yacanka, meyasa kike zama da datti ne
haka,Joda kam tagumi tayi tana kallon sa duk
yanda yaso takar bamasa amma taki, yana fita
kuwa yawuce supermarket yasiyo mata sabulun
himalaya tareda mansa dakuma tiraren smart
collection,
yakawo mata joda tayi godiya aranta kuwa tace
ina ni ina wann sabulun mai kamshi ina wanka
dashi zasu tsigeni idan sukaji kamshin sa ajikina
haka takaisu daki acikin akwati ta ajiye bata
sake waiwayarsu ba , mansura kam abu yafara
damunta yau kwana uku Ahmed yaki kulata sedai
su sha fira itadinma ita kadai ke zuba bada shiba,
idan ta tabasa komai baya cewa , gashi amatse
take koba komai tasha abubuwa barekuma yanda
take da bukata Yau kam tasha al'washin
nemamsa da kanta domin kuwa bazata jure
hakanba, Ahmed kuwa yana lure da take2 ta shi
isa yamata banza
arayuwar shi yana son mace mai al kunya da Jan
aji , bayan sun gama dinner sunyi kallo kusan har
12 mansura tacanza tasha zuwa wata ta shar da
ake sako BF, aikuwa tayi sa'a ansaka wani, tuni
tafara murmushi aranta kuwa tace yanxun zakaji
feelings. Ahmed kuwa yi yayi tamkar bai gane
komai ba , seda tamatso a kusa dashi tafara
romancing dinshi, sann yadaka mata tsawa miye
haka? Dallah kicire mun wann iskancin kawai zaki
sa mutum kallon haram, mansura tace hava dear
duk kauce war danake kaki kagane iye, yau
kwana biyar ace babu wani abu da muka gudanar
amatsayin mu na ma'a u rata ,
Ahmed yace ohhh....ay seki fito fili kigayamun
cewa namiji kike bukata ba kizo kina kunna mun
bf ba kokuma a zatonki shi zaisa nakulaki ,
mansura tace sorry dear yanxun muje daki,
Ahmed ya ballah mata harara muje daki inmiki
ubanme acan, mansura ta kimtse fuska tace
kabani hakkina, Ahmed yace hakki koh? tobanga
dama ba, sena tashi yana kai nan yafita , haka
mansura ta kwana daddafe da mara tsananin
sha'awar datake ji, Ahmed kuwa tin safe yafita
domin baya son wata maganar Mansura nafitowa
taga baya nan, tsaki tabuga ni wlh bazaka
kasheni ba da lfy na wanka tayi ta sauya
kaya.........
Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours ago
Pharidah Ahmad
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�1鈨�
tazare key din motar ta se zaky hotel, tana kae
tasa Kiran sabon saurayinta kamal, shikuma
dama yana expecting kiranta tinda sunyi dashi
2ydx idan angon yafara , haka yaxo yasameta
suka aikata masha'arsu, kamal yace sury kin jiki
kuwa billahillazi kinfi korama kinji yanda naji
sama na yawo dani,
mansura tace dole nefa kasan nasha gyara
kamar mutuwa shikuma angon Dan apixy ne "
baitashiba gara kawai na nema Dan bazan iya
koda sati dayaba batareda naji ehem ba, kamal
ya kyalkyale da dariya bakida dama Karfe 1 dae2
tadawo gida tasake shiri sann tafito parlor domin
tasan yanxun Ahmed zaizo,
amma shiru ba labarin sa, bai dawo gida ba se
guraren 11 yana xua ya hau dinner bayan
yagama yaxauna parlor , ganin fuskarsa adaure
yasaka mansura low tasan tin abun jiya ne "
wato kar nasake tambayarshi koh " ay nasan
maganin ka Daki taje ta dauko wani caset, da
kakanta yabata wa'azin gombe ne " tasaka
ananan suna saura re Ahmed dae baice kala ba ,
se gashi ana fadan hukuncin Wanda yaki bawa
iyalanshi hakkinsu alhali yana qlw, da matar da
ta guje mijinta,
Ahmed yakalleta yaga shi take kallo, tsaki
yabuga yabar gurin se dakinshi wanka yayi
yasaka jallabiya sann yadawo parlor koda yazo
har tafara bacci, bubbugata yayi firgigit tafarka ,
kisameni adakina yafada kawai seya koma ,
mansura tayi jugum tomeni Allah yasa dae
kudine zai bani da wann tunanin tabisa baya ,
suna shiga Ahmed yarufo kofa yanuna mata
gado, ba musu mansura tazauna, Ahmed ya
kashe light din. aykuwa gabanta yashiga dukan
uku Mansura tace lfy Ahmed menene, Ahmed
yace hakkinki zanbaki tinda kinkai karata agurin
Allah.
mansura tace no wlh bahaka bane Dan Allah Kayi
hakuri kabari se gobe ni yanxun ban shirya ba
kuma bana Jin dadi, Ahmed yace ni dinma bashiri
ne daniba amma naga alamar ke zaki iya kauce
hanya idan baki samu biyan bukata ba , mansura
tafashe da kuka na shiga uku, Ahmed kam ko
sauraran ta baiyi ba yashiga aykinshi ayadda
yake sarrafa ta kadae yasaka ta manta dawani
abun, Ahmed kuwa yakudurta aranshi Yau seta
rana kanta har kusan 3 bai wani abu ba, mansura
kuwa tasha gurza tin tana nishi har tafara kuka
yanda yake mata ne basauki ,
lokacin da yafara ibadar aure kuwa ihu take
kamar zata shide Ahmed kuwa bai mata a sauki
ba kuma yaki saurara mata, har kusan safe abu
guda ake seda yamata lissss ko yatsanta bata
iya dagawa sann yabarta yaje yayi wanka
yawuce masallaci yabarta agurin , yana dawowa
yaganta a yanda yabarta wata irin tsawa yadaka
mata seda tamike zaune bata shirya ba, Ahmed
yace maxa kificemun adaki kafun nayi miki Dan
baxan Duka fasika jahilar yarinya
Sanin dalilinsa na kiranta fasika baisa tayi
kokarin cemasa kala ba illah kawai tafita adakin
dakyar take takawa tsabar azabar dataji, kusan
kwana uku tana jinyar jiki Ahmed kuwa bai sake
bi takanta ba, dukda baya ganinta, mansura takira
hjy tayi mata bayani, hjy tace ay kinga irinta ke
wlh shegen kwadayin tsiya gashi duk kudin da
muka batar sunje abanxa, mansura tace Allah
anty bakiji yanda naji bane bana iya jure
bukatata
Hjy tace to ay ga abunda kika jamana nan, nan
talabar tamata yanda suka maida joda, tuni ciyon
ta yabace, mansura tace kae amina shegiya ce,
tamun dae2 karku bari yagane kuma karku
sakata ayki agabanshi, hjy tace ay bama zai gani
ba wlh haka nake son ji, kinga ma naji yana waya
da Mahmud cewa wae zamu je Egypt honeymoon
kafun mu dawo tazama kiyashi gabadai suka sa
dariya...........
Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours ago
Pharidah Ahmad
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�2鈨�
Joda tagama gyaran dakin amina dana hjy sann
takoma yimusu wankin underwears, danko har na
hjy itake wankewa, joda tana wankin pants din
hjy kawai seta saka dariya, tace yoni wai duk
wann wake ken wandon duwawu ke
cikashi....nima dae asea abun yabani dariya
Ashe afili take zancen kawai taji ana fadan
duwawun uwarki shegiya , joda ta tsorata dajin
muryar hjy, danko tasan makomarta abi kadan
tayi setaci Duka bare kuma irin wann subul da
baka , tsawo ne mai kauri tasaka tadinga dukanta
seda ta mata liss sann tabarta tsabar tasaba da
Duka ko kuka batayi, tagama aykin ta tsab
dasauri ta tsere batareda tasanar tagama ba,
tana xua tasame gwaggo zaune tayi tagumi, joda
tace hey gwaggo lfy? gwaggo tace ina lfy joda
narasa meke damunki duk kinbi kin canza
Joda tayi ajiyar zuciya tace gwaggo lfy na qlw ki
sakani a addua, gwaggo kam seta fashe da kuka
joda ma haka ba mai lallashin wani acikinsu ,
Mahmud ne ya katse musu kuka, dasauri gwaggo
tajuya ta share hawayenta, Mahmud yagaida
gwaggo sann ya dubi joda yace yadae yar kanwa,
joda takirkiro murmushi tace qlw yayana,
Mahmud yace gurinki naxo gwaggo , gwaggo tace
nikuma Ince dae ko lfy? Mahmud yace qlw
gwaggo se alkhairi
Gwaggo tagyara zama, joda kuwa tamike zaune
domin tashi, Mahmud yace a'a yi zamanki joda,
takoma kusaga gwaggo tazauna, Mahmud yace
gwaggo gidanmu ne anmatsamun akan nafidda
matar aure musamman da aka ga Ahmed yayi
aure, nikuma arayuwa ta babu wadda nakeso
kamar joda tin kuna yan DAJI gwaggo tace ayya
Mahmud dacan kana sonta kaja baki kayi shiru ,
har aka maka riga ye
Mahmud yace bangane rigaye ba, gwaggo ta
zayyane masa zare da abawa , dogon nishi yaja
tare da hawaye har cikin zuciyarshi yaji kishin
Ahmed , Mahmud yace dacan Ahmed yasan da
auren kuma yakara mata? Gwaggo tace au dama
itakadai akace ya aura ne " Mahmud yace gsky
gwaggo joda matar mutum daya ce sann bata
cancanci rashin kulawa ba , naso ace ni aure ta
domin in zame mata gata , gwaggo tace hakuri
zakayi Mahmud Allah yahada ka da wadda tafita
ameen "
tin da suka fara joda take kuka , meyasa nake
samun masu sona tsakani da Allah amma anace
min akan Wanda baya sona, sekuma takara
fashewa da kuka, Mahmud yashiga lallashinta
dakyar tahakura, yana fita Sega khalthum taxo ko
kallon joda batayi ba taje inda gwaggo takai
mata korafin joda , gwaggo tace nikaina narasa
gane kanta dazaran na matsa mata kuka take
sakawa, khalthum tace kodai aljanu ne suka
shafeta, gwaggo tace to waya sani nibanga
alamar aljanu ba kawai abunda nafahimta akwai
wani abu dayake damunta bata san fada keda
kike kawarta kexaki san kome nene
Khalthum tace nayi2 gwaggo taki sanar dani
komai, abun nabani tsoro yanda joda tazama
kamar wata kaka , abun se an hada da addua,
mansura taxo gun hjy gaishe su tareda musu
bankwana, anan tasame joda na goge2 mansura
tace keee biyoni toilet ki wanke mun kafa na, ba
musu joda tabita toilet mansura tamika kafa joda
ta wanke mata tanayi ana mata ran kwashi wae
zata balla mata kafa , tana gamawa takoma yiwa
hjy guga aykin datake agidan har yazarce
tunanin mutum,
Karfe uku Ahmed yashigo gidan, direct dakinshi
yaje yakwanta baitashiba se kusan 4:30 dajin
motsinsa , mansura tace wa joda taje takai masa
abunci , cike da fargaba taje dakin bata ganshi
ba Dan haka tayi gurin table din dakin ta ajiye,
bata Ankara ba taji ta tayi tintibe da mutun
aykuwa abuncin ya bare Akansa tuwo da miyar
kuka , taji dad dawa , Ahhhh......naji Ahmed
yafada dasauri joda taja dabaya , fitila yakunna
Dan ganin waye. Ahmed yayi toilet Dagudu
yadunga sharara amai kamar zai a maye
hanjinsa, joda takara tsorata tashiga kwashe
abuncin ,
Ahmed kuwa wanka yayi kamar zai yi wankan
zallar tirare ajikinsa, yana fitowa yartada joda na
goge gurin, keee ubanwa ya izoki da wann
abuncin adakina jikinta narawa tace anty
mansura ta amina su kace nakawo maka, Ahmed
yace ke kuma Dan ubanki sekika zo kinga namiki
kama da mai cin tuwo da wann shegiyar miyar,
joda tace kayi hakuri, abunda yatsana kenan,
cikinta yayi yacabko rigarta amma tsabar tsamin
jiinta yasa kashi sakinta, joda ta bare baki xua
kuka carab a idon Ahmed yellow teeth dinta suka
masa arba da wani warin daban aykuwa Ahmed
anan yadin ga kwara amai harda su shesheka
Joda tafito dakin aguje, tayi inda gwaggo ,
Ahmed kuwa yana gamawa yasake wanka
arayuwarsa baitaba tsanar abu kamar yanda
yatsani joda ba musamman a yau, parlor yafito
fuskarsa ba annuri , amina! mansura! Haka
yakwala musu kira atare suka zo, seda yagama
yi musu kallon wulakanci sann yace wato Dan
kun rai nani zaku ay kamun tuwo da miyar kuka,
amina tace tuwo kuma wayayi tuwo agidann
Ahmed yace ubanki ne yashiga tsula mata belt
mansura tace hava Ahmed meta maka aykuwa
yahada su subiyu ya dinga Duka yana ball dasu
yanata hada kansu yana bugawa tuni
kowannensu tafidda jini, hjy tafito dasauri tarike
masa hannu itama ya wulgata gefe seda
yasumadda amina mansura kuwa da alama
yamata targade a hannu.......
( please masu cewa ina Jan aji akan novel dina
kokusa bahaka bane. Kurika uxuri akwai aykin
gida ga karatu, sann yanxu lokacin biki ne
munata lalura idan nasamu tym wlh bazan kiyin
typing ba, kuma kunfi kowa sanin typing akwae
wuya, abunda zan gaya muku idan nayi yau
baxan yi gobe ba sbd rai nason hutu , please ayi
hakuri da tsarina 馃憦馃徑 )
Muje zuwa
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/29/16, 12:09 AM - Queen Safiyyert馃憫: FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�3鈨�
Joda tafito rike da boket zatayi shanyar tufafi,
Sega Mahmud yaxo gidan ko kallonsa batayiba
ta cigaba da aykin ta. Mahmud yamatso yace
mata, kanwata karki damu zan same Ahmed muyi
mgn in har baya sonki tokuwa ya sauwake miki,
joda tadago idonta dasuka cika da kwalla tace ya
Mahmud kana ganin zai iya, baya son farin
cikina, ya rantse seya dauwamar da bakinciki
arayuwata sedai Allah baya bacci bare
gyangyandi Allah zai saka mun , Mahmud yace
no joda kar yiwa yayanki mijinki Allah ya isa
Joda takallesa ta girgiza kai sann tawuce
tabarsa, Mahmud yayi jugum koshine dalilin
dayasa duk tabi ta lalace batada wani sukuni,
direct gidan Ahmed yaje, yakirasa awaya, Ahmed
yace tokashigo mana kokuma sena maka iso
sekace baqo, Mahmud yashiga har dakinsa,
bayan sun gaisa yace Ahmed yanxu ashe har
akwai abunda kake boye mun, Ahmed yace
dakata inada aure bakasaniba shine zancen koh "
Mahmud yace yes amma hakan da kayi kayi
dae2 ,
Ahmed yace to menene amfanin gayama ka
bayan kana son yarinyar, Mahmud yace aykuwa
daka gayamun daban bari sonta yayi zurfi a
zuciya taba, Ahmed yace ohh....ashe hakane,
Mahmud yace Ahmed al_hakika bakaine mijin
dayace da joda ba Sam baku dace da Juna ba
joda na bukatar mai lallashin ta mai kwantar
mata da hankali bamai wulakantata ba kamar kai
Ahmed yace dama wann ne yakawoka? Mahmud
yace kwarai dagaske naxo karba mata yanci ne
either ka maidata gidanka kokuma kabata
takardarta inhar kasan bazaka iya xama da itaba,
Ahmed waxai kawo wann kazamar kucakar
yarinya agidansa yarinyar da ko.....sekuma yayi
shiru,
Mahmud yace kadaiji tsoron Allah, Ahmed yace
dama wann ya kawo ka gidana ? Mahmud yace
ehh shine yakawo ni, Ahmed yace please get out
tareda nuna masa kofa b4 kowa yaji mu agidann,
Mahmud yace idan ba'a fita dinma saime, Ahmed
yace wlh kasan abunda zan iya da wanda baxan
iyaba so mind yourself
Haka sukayi challenge daga karshe Mahmud
yabaro masa gidansa, yana fita Ahmed yafauko
eviron drink yasha sann yaji relief " Mahmud ya
fito kofar gidan anan sukayi karo da amina zata
gidan kallon kallon suke yiwa junansu daga
karshe amina tajuya dasauri tashige gidan,
Mahmud yace fine gul inaga nan zan maida
sheqata , tin daga ranar yake Jin feelings akan
amina itama haka dayake Mahmud akwai kyau
kadan Ahmed yafisa , gidansu yake xua kullum
gurin garden anan yake haduwa da amina amma
sedai su yiwa Juna kallon kallon amma ko
gaisawa basayi
Yau kam Mahmud yaci al_washin yi mata mgn
bayan yazuna yafara kara tin jarida Sega amina
tazo wucewa, Mahmud yace jimana, amina
tajuyo tana masa wani kallo, Mahmud yace
mezai hana mufitar da sakonnin dasuke
zuciyoyinmu , amina tace kana da saqo ne danni
dae banida shi, Mahmud yayi murmushi yace I
have mssg, I love you daz oll na kwana2, amina
ta kyalkyale da dariya lallae kayi kokari............
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�4鈨�
Daga ranar soyy tabar ke tsakanin amina da
Mahmud kudi yake kashe mata kamar me, shi isa
ta makale suka samu nonon ta tsa, joda nakule
dasu kishi fall aranta dukda tasan tanada aure
kuma bawani dating suke ba amma tana Jin
kishin sa aranta, jama'a kuji joda
Yaude su Ahmed anvar Nigeria, yaune kuma su
joda zasu fara exam karatu take bakama hannun
yaro, Sam bata kula da yanda jama'a ke hanta
rarta, karatunta take ba ruwan ta har Allah yasa
suka gama WC, agida kuwa tanan amatsayin
boya se abunda yakaru Wanda yasan joda baya
ganeta a yanxu sedai yayi la'akari da muryar
Rayuwa suke ba laifi a Egypt mansura bata sake
neman Ahmed ba shima haka, kuma ba abunda
yake nuna mata sedai tafahimci mayen boobs ne
idan tayi kwalliya sukadai yake kallo hakan yasa
takara yin shiga kala sometime baisan randa
yake tabawa ba seyayi nisa kuma seya tura ta
gefe abin na damun mansura gashi batasan kowa
ba bare tabiya bukatar ta gashi tana tsoron sake
tinkarar Ahmed kar yasake gurzarta kamar kayan
wanki
Muje zuwa gobe zan cigaba zanyi page 4 "
banda complain please, bakusan uzurina ba
Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours ago
Pharidah Ahmad
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�4鈨�
Ahmed yafita siyo musu abunci, joda yadawo
mansura na dakinta yafi minti biyar baigan tazo
tarvonsaba, hakan yasa yashiga dakin, kana gado
yasameta a dukul qule se wani nishi take, Ahmed
yace lfy dae ko? Mansura tace marata yake ciyo
Ahmed, Ahmed yace ohhh....sorry month dinkine
kenan, mansura tace no Ahmed bashine neba ,
Ahmed yace to menene kinsamu ciki ne koya?
Mansura tace nima bansaniba plss help me,
Ahmed yace with what? Mansura tafashe da
kuka, wlh Ahmed kana cutuwata, kasan menake
nufi amma seka saka nafada sann
Ahmed yace mekike nufi, mansura tace
bansaniba aciki tsawa, Ahmed yazare ido nikke
yiwa ihu? Mansura tace ehh anyi kayi duk abunda
zakayi Ahmed yayi kadi da hularshi yabita kan
gado ya cakumi wuyanta dagota da zaiyi blanket
ya zube akasa bakomai ajikinta, Ahmed yabuga
tsaki sgegiya mayya kawai randa nake bantaba
ganin mace jarababbiya ba irinki ke kinma guce
harija wlh , ni Sam baxan iya daukar hakan ma,
ko abinci yana kosadda mutun bare mace,
mansura tace nadaijiya join me kawai, Ahmed
yabuga tsaki , kindai San aure na mutuwa akan
hakan al qur'an idan kika matsamin kotu ce zata
raba aurenmu
Sam bana iya wann jarabar , mansura tace okey
ayi timetable. Ahmed yace bakida hankali wlh
timetable sekace a skull, dahaka dae tashawo
kanshi sedai koyau ta gurxu, aranta tace kowani
irin karfi ne da Ahmed oho shi Sam baya gajiya
bare ya kasa tashi sekace wani inji, tin ranar
tsoron nemansa takeji aykuwa tafara zancen gida
tinda bawani yawo suke ba bare tasamu ta tsere
tanemi wani awaje , Ahmed kuwa yace se sunyi
2month zasu koma gida
Note.....wann isuwar page din jiya ne danayi
kadan. Okey....?
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�5鈨�
Alhmdllh su joda ankammala paper lfy sedai
fatan nasara aciki, suna waya da hafsa dinta
sosae har ta labar mata zancen amina da
Mahmud, baqaramun rudu hafsa tashiga ba,
sedai taboyewa joda bata son agane tana son
Mahmud daga ranar tashiga damuwa karatunta
ma duk yaja da baya , taqaqu hutunta yaqare,
joda kuwa nanan yanda take se abunda yakaru,
Mahmud yayi iyakacin kokarinsa amma yakasa
gyara ta dole yasaka mata ido " gwaggo kanta
tadena kulata abubuwa duk dunbi sun mata yawa
gashi tadena samun wayar doctor bare tagaya
masa halin datake ciki shikadai yarage mata
masoyi, khalthum , gwaggo, Mahmud duk sun
guje ta , batada wani hutu sena ayki idan ta
kwana tokuwa dare ne yayi asuba nayi sallah
kaday take watarana ko karyawa batayi za'azo
nemanta haka rayuwar ketafiya ba dadi agurin
joda, hjy kuwa da amina sunma daina kulata
saboda ta rigada tazama yanda sukeso
Wata daya da tafiyar su mansura, joda takamu da
ciyon kazuwa, gakuma kwarkwata akan ta, su
kansu su hjy kyamarta suke dole su kace sun
dauke mata aykin kafun taji sauki suna tsoron
kwasar cutar, gwaggo tafidda ita waje tana mata
ferfita, Sega hjy binta tazo dasauri gwaggo taje
ta tarveta tana mata sannu da zuwa, amma Sam
hankalin ta na gun joda tace gwaggo me
yasameta ne haka, gwaggo tace oho gata nan
kitambaye ta , hjy tace gayamun joda kinyi
wanka da ruwan gulbi ne kodai wani kwaro
yatava ki
Gwaggo tace kodaya tsabar zama da datti ne da
rashin wanka, hjybinta tace bangane rashin
wanka ba joda dana sani tsab2, gwaggo tace
asaninki nada ba, hjybinta tace joda ke kuwa
meyasa zaki jawa kanki bala'i haka keda kika fito
daji bakiyi wann ba seyanxu dakika zo birni,
birnin ma capital city . joda tafashe da kuka,
tace wlh ba laifi na bane su suka sakani hakan,
hjybinta tace su waye ?anan joda takwashe
komai tagaya musu duk wahalar dasuke bata
Take idon gwaggo yacika da kwalla shine baki
taba gayan ba, joda tace sunce zasu ballani idan
nagaya wa koda tsuntsu bare mutum, hjybinta
tace to menene silar hakan, gwaggo tabata
labarin komai tin zuwansu har auren ta da
Ahmed , dakuma zumuncin su, hjybinta tayi
murmushi kice alkhairi ne yakawoku nan, ayko
joda kinyi miji, shi isa suke miki hasada , ina
matar Ahmed zata zauna da datti Wanda baya
san ganin abun kaxanta ko kadan, yanxu yanda
za'ayi, ki hado mun kayan ta tsab, banda
wadanda tasaka acikin wann aykin sababbin
kawai zanje da ita gidana bayan munje asibity
angama kula da ita tinda bai fito dayawa ba
Gwaggo tace ayi haka zaki dorawa kanki nauyi,
hjybinta tace bakomai yayarki margayiya saratu
bamaijin kanmu kodanta zanyi haka, haka kuwa
akayi gwaggo tayi yanda tace, sann tace karta
gayawa kowa cewa ga inda joda take kice musu
Dan gin mahaifinta suka dauketa har taji sauki ,
gwaggo tace insha Allah. bawanda xaiji Allah
yasaka miki da aljanna mafificiya ameen
Meena hospital aka kaita kwanan ta shida sann
aka bata sallama jikinta yawarware sosae, suna
dawowa hjybinta tasaka aka hada mata sabulun
wanka mai kyau sann aka tsefe kanta aka wanke
shi Tass aka yi kala ba hudu, haka hjy binta
tasakata a toilet ta gurjeta son ranta da soso
Sega joda anfara haske ,haka aka dawo kan
teeth dinta tamkar dae wata yar kauye komai
seda aka maidashi sabo, kullum da sabulu mai
kamshi take wanka ga turaruka, tasha dilka da
kulacca,
Sati uku joda tazama balarabiya nikaina tsoro
take bani yanda tadawo kamar ba itaba jikinta
kamar auduga, gashinta aka shiga gyaran shima
ba laifi yadawo , hjybinta bata bartaba seda taga
tadawo dass da ita sann tadawo teaching dinta
akan yanda zata ja hakkinta akan mijinta da
kuma su mansura , fita take da ita gurare da
dama tana ganin abubuwa, yanda rayuwa ke
tafita ana haka joda tace mota takeson koyo hjy
tayi matukar murna dajin hakan............
Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours ago
Pharidah Ahmad
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�6鈨�
Aykuwa tuni tafara koyo dayake joda akwai kai
nan danan ta iya, tayi wasu kawaye a unguwar
samira dakuma yuhana wadda take christa ce, da
taimakon su joda takara wayewa , waya gwaggo
ta aykomata wadda dad yabata dadewa, iPhone
ce mai kyau, yuhana itace ke koya wa joda waya
tabuda mata wp , fb imo, soma, Instagram,
snapchart, dasauransu, joda kam kallonta kawai
take tinda batada numbers din kowa , a hankali
har tafara iya yiwa kanta komai make up dama
light kawai take yi, amma seya karbeta
Watanta biyu agidan ta waye sosae tadauki
manners dayawa agurin samira da yuhana,
barinma yuhana data koya mata yanda zata ja
apixy da kuma yanda zatayi mgn atake ta basu
lbrn ta tsab hakan yakara sakasu suka bata tips
dayawa akan Ahmed da matarsa, aykuwa joda
taji harta kaqu takoma gida sbd tara ma zalunta
da a kaci , magana wann da kwarkwasa seda
suka nuna mata yanda zatayi
Su mansura andawo Nigeria murna gunta ba'a
mgn, gidan su Ahmed suka sauka ansha
delicious kala2 Ahmed kuwa dakinsa yaje yayi
baccin sa mansura kam wanka kadai sukayi
tacanza kaya suka yi gurin malaminsu, magani
aka bata Wanda idan tasha alawar zasuyi kiss
matukar hakan tafaru tokuwa komai takeso zata
samu agurin sa ko nawa tayi tambaya zata samu
agurinsa ba gaddama da murnarta tadawo gida
Yau kam joda ta matsa gida takeso tana son
ganin gwaggonta, mota hjybinta tafiyar mata
sabuwa gal fara kirar jar chavarolet, acikin gadon
mahaifinta murna gun joda ba'a magana, wanka
tayi tasaka prom gown green da ratesen black
tayi parking gashinta atsaka yazubo har gadon
bayan ta rolling kawai tayi ta dankwali tayi light
make up sann tasaka katon madubi Wanda
yakara fito da ita ga takalminta heel shoes
kamfanin prada, se yar jakarta wadda tada ce da
shigar
Tana fitowa hjybinta tasa shewa woww yata kin
ganki kuwa, har mota yuhana da samira suka
rakata sann tajata se gidan horn uku sann aka
bude mata gate din direct tawuce gurin parking
din motoshi kuma gurin da Ahmed ke ajiye motar
shi inda yataka mata kafa , horn tabuga dakarfin
tsiya kasancewar ta hango Ahmed a gefe yana
shan iska, Jin horn yayi yawa yasaka mansura da
amina gamida hjy fitowa domin ganin waye. tafi
minti goma kafun ta fito a motar tana chrt dinta
tamkar bazata fitoba shikanshi Ahmed yakagu
yagan kowane ne kaddara takaishi gurin
Joda tabude ganbun motar ta zunburo kafafun ta
taki fitowa Ahmed yatsurawa kafafunta ido kamar
bana mutum ba, nanma tadade kafun tafito sann
tafito gabadai batareda tajuyo sun gantaba,
amina tace wai waye wann sekace yar shugaban
kasa wann shegen apixy, dakyar joda tajuyo,
tadau minti uku sann tafara tako dass dass
kamar hawainiya tanata zunburo baki kamar mai
shirin daukar selfie, gabadai mutuwar tsaye
sukayi danko basuma gane ko wacece ba hjy
tace Allah yasa dae amina ba saurayinta kika
kwace ba bashakka wann yar shugaban kasa ce
Seda takawo gab dasu sann tacire glass tana
musu wani irin kallo, a hankali tace hello, sann
takalli mansura data mutu atsaye danko kamshin
joda kadae abun firgitarwa ne " joda ta matsa
mata kumatu yade in law, na sameku lfy? tana
kai nan tayi wani juyi dogon gashinta yamari
mansura, takara rike kumatu kasa tayi dasauri
amina ta janyota.............
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�7鈨�
Tin a kofa tafaran gwaggo na gwaggo na zoga
jodanki really miss you my cweet mother, hjy
tace shikenan wlh itace ayko wlh sedai idan
outside taje tayo wann wayewar duk ma wata
nawa kuma yarinya tadawo dawani fitsara harda
su mota, lallae Ahmed muna fuki ne
Ahmed kam mamaki yacika shi yarinya daya bari
kamar kayi amai itace haka kamar wadda tayi
rayuwa aturai, lallae da sake, kuji Ahmed pah
馃憟馃徎 gwaggo kam bakinta yaki rufuwa ganin
joda tace lallae hjybinta ta iya kiyo kinganki kuwa
joda tace Allah koh gwaggo? Yanxu na wuce ayki
bare hantara, matar big bruhh dole abini a sannu
sann nice uwargida, gwaggo tace kiyarda da
auren kenan, joda tayi wani shu'umin murmushi
nayarda mana gwaggo
Xua anjima kadan tayi wanka tasaka riga da
wando leggings sann ta tubke kanta guri guda ,
tanufi parlor gidan, TV ta kunna tayi zaune tana
cin apple. Sega amina tafito amina tace kee
ubanwa yakawoki nan harda su kunna TV, joda
tace kinsan Allah aminatu idan kika kara kiran
sunan ubana sena fasa miki baki, amina tace
kam nizaki mara wlh kuwa dako ubanki dake
lahira seya ji kukanki dasauri joda takai mata
mari aykuwa anan suka dinga ko kuwa
Hjy da mansura suka fito aguje suka rabasu, hjy
tace ke ubanme kike a parlor dinmu da har zakiyi
danbe da ita, joda tace myb ubanta ne silar zuwa
na parlor dinn domin shi ne ya daura mun aure
da dansa, dae2 nan Ahmed yashigo parlor, hannu
wansa yarungume yana kallonta yanda take
musu iskanci , Ahmed yace ke lfy? Joda tayi
tamkar bata jisaba , Ahmed yace ba dake nake
magana ba, joda tadaga masa hannu wait bada
kai nake ba ay xanxo kanka, Ahmed yazaro ido
yana kallonta , tace hjy kiyiwa yarki gargadi akan
ambaton sunan ubana inbahaka ba takusa rasa
hakoranta
Ga hanya amma tabi tsakanin mansura da hjy
zata wuce mansura ta cabko ta ina zaki, joda
tace sake ni kona balla hannun. ....kujimun joda
kamar wata kakkarfa " mansura tace sekin
gayamun inda zakije, joda tace dakin mijina zanje
kozaki hana, mansura tace waye mijin naki
yaushe ma ya yarda cewa ke matarsa ce, joda
tace ohh....wann kuma shi zaki tambaya baniba,
mansura tace bakisaba wlh ba inda zakije,
yaushe kika tare agidann bare har ki isa shiga
dakin miji
Joda tace wann kuma yarage naki yaudae kwana
nane dukda banida interest da kazamin gidanku
amma nan dakin komai shi bai isaba tana kai nan
tafice , Ahmed yadaka mata tsawa ke gidan
ubanwa zaki, dasauri tasakata amma seta basar
tace idan ka biyoni kaji " Ahmed yace metake
nufi zanyi maganin wann kwailar
Akan gadon sa yasa meta tana wakar JustinB,
Ahmed yacakumo wuyanta ke ubanwa ya izoki
kimana rashin kunya, joda tace no no it's my
time kunyi naku yanxu kuma ni nakeyi Ahmed
yace keee nikike gayawa magana , joda
ohhh.....na manta ur my husband koh " Sega joda
kasa sannu da xua oga na, Ahmed yafusata ya
janyota dakarfi suka fada kan gado , ido suka ku
rawa Juna dasauri joda takauda idonta bazata
jure hada ido dashi ba sun dade ahaka sann tace
ay dai seka matsa mun kawani hayeni
Da sauri Ahmed yadaga mata, yace to ay seki
fita adakina, joda tace wlh ba inda zani yau bacci
nane adakinka zan kwana, Ahmed yace wa yace
miki haka , joda tace tin randa ka aureta nake
kidaya bantaba mantawa, Ahmed yace
ohhh....dama kina son tarewa ne abaki hakkinki
kenan, joda tace tuppp mekake dashi dazaka
bani.......
Muje zuwa
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 10 hours ago
Pharidah Ahmad
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�8鈨�
Ahmed yakwabe mata baki aykuwa tasa kuka
tanata bubbuga kafa, ni wlh ban yafe maka ba,
Ahmed yace ni kike yiwa Allah ya isa, joda tace
ehh....ni ay marainiya ce amma baka dubi
maraicina ba ka dinga zaluntana kana kyamata
kana kushe halitta na goma muka hadu seka
cuceni
ni wlh banyafe maka Allah zai......bata karasa ba
Ahmed yarufe mata baki, ni yayanki ne bazan
cucekiba nan gaba kadan zaki gane dalilin hakan,
joda tabuge masa hannu tuppp Allah sauwake
kazama yayana sedai yayan hafsa baniba wlh , ni
Mahmud ne yayana bakai ba se abdallah sukadai
suke tausayina,
Ahmed ya bata fuska yace wlh wlh wlh, nawa
nayi joda tace u..u uku ne muryar ta narawa
yace gud idan nakara jin sunan abdallah ko
Mahmud a bakinki se kinyi nadamar sanin su
arayuwa , yana kai nan yawuce yabarta atsaye,
tana hawaye, yunwa takeji kuma tasha al washin
anan zata kwana ,Ahmed kuwa bai sake bi
takanta ba yayi gidansa yabarta anan joda kuwa
tashiga yimasa bincike har taga cornflakes na
chocolate aykuwa
da murnarta tadauko shi tahada abunta tasha
sann tayi sallah tabi lafiyar gado ,bata farka ba
se kusan asubah mamaki yacika ta ganin anyi
mata rufa da blanket , sann anrage sanyin AC da
fanka, alwala tayi sann tayi sallah sann ta hada
tea tasha kasancewar akwai komai adakin,
baccinta takoma se 8:30 tafarka brush tayi sann
tawuce dakinsu inda gwaggo
Gwaggo tace kewai ina kikaje ne naga Ahmed
yafita shikadai jiya, joda ta sosa kai gwaggo
shine yace duk ran girkina dakinsa zan kwana,
gwaggo tajuya tawuce tana dariya sann tace
Allah yakyauta ameen " agurguje tayi wanka
tashirya cikin atampa red nd blue tayi daurin Dan
kwalin ta Ali_yaga_Ali , se purse dinta red
takalmin ma red flate shoes tazuba tiraren nan
basauki light make up ne tayi tazubo gashinta
har gadon bayan ta .
inda gwaggo taje tace mata zataje gidansu
khalthum, gwaggo tace kin nemi izinin mijinki
Joda tace zamuyi waya after yanxu sauri nake,
gwaggo tace kitabbatar baya fada, joda tace
koma zaiyi wann yarage nasa ba'a gida sa nake
ba bare yasaka mun gate , gwaggo tace kidaiji
tsoron Allah ko a ina kike aljannarki akafarsa
take, joda tace bara kuma yatake ba yahani ni
shiga, tana kai nan tazare key din motar ta tayi
gaba, gwaggo tace ohni manga Allah yashirya
mun wann yar
Wakar gfresh take sha kano to califonia tana
mamin abunta dae2 wani titi ta tsaya
kasancewar motoci sunyi yawa, zata daga Sega
wani yaxo aguje yasha gabanta hakan yasaka
yabugi motarta har yafsa mata gaban mota, joda
tace kambuu, dasauri tasha gabansa tafito sanye
da katon glass dinn tana tauna alawa, tace kai
mahaukacin inane dazaka fasan mota sann kaki
bani hakuri kawuce
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�9鈨�
yaron yace keee kinsan koni waye kike gayamun
mgn , joda tace Allah yasa kaine Dan sarkin
makka baka isaba, yaron yace ke karki kawomun
rashin kunya yanxu zanyi maganinki joda tace
kodai nayi maganin ka ba, yacee kewai yar
ubanwa ne " joda tace yar ubanka matar soldier
idan kamun zancen banza wlh yau seka kwana a
S,
Ahmed dake gefe duk tacika shi da mamaki
aranshi kuwa yace duk ina tsoron yarinyar nan
yaje dubi yanda ta yafa mayafi akan kafada
kuma tafito atiti tana challenge da wani dole
yadauki mataki akanta, joda tace ko kana musu
yanxun sena nuna maka waye, hannuta tanuna
dae2 motar Ahmed batareda tajuya ba,
Ahmed yazaro ido danko baisan taganshi ba ,
yana Saye da kayan soja, dasauri yaron yace
plss sorry madam dama ke matar oga Ahmed ce,
joda tace kwarai dagaske , to Dan Allah kiyi
hakuri, joda tace sekayi kneel down. dasauri yayi
joda taja masa kunne sann tace be more careful
okay?
tana kai nan ta maida madubinta tashige motarta
batareda takalli Ahmed ba, shikam dariya tabashi
wann acting din nata kamar a film mace amma
tana wani irin abunda bakowane namiji keyi ba ,
sewani iskanci da rashin kunya takeji, Ahmed
yace towai kuma harda proud ita matar soja,
yace zaki gane ke matar soja ce idan kika shigo
hannu
Daga nan se gidansu khalthum, maman khalthum
tasama a parlor tana cin abunci, joda tace gunta
dasauri ta rungume ta, mama tace kaikai wacece
zata idani haka, Joda tace yarki ce mamana,
mama tace Ahhhh.....joda kece, khalthum jin
ance joda tayada plate ta ballo aguje tarungume
joda, tana wayyo Allah nah joda na kece kuwa
ina kikaje, joda tace ayseki sakeni tukun sann kiji
komai ,
khalthum tajata kan kujera suka zauna, khalthum
tace joda ina kikaje kika barni, joda taballah mata
harara dama kina sona kika kyama Ceni,
khalthum tace wayyo joda na wlh bahaka bane
lamarinki ne abun tsoro nima ba'a San raina
nabarkiba a sedan kawai bana iya kallon ki acikin
wann halin "
joda tace aykuwa masu iya kallona sun neman
mun magani , khalthum tace kigayamun mana ,
nan tabata labarin komai, khalthum tace kan"uba
wato so sukayi su kasheki da ranki , allah yafi su
mama tace seki dage da addua irin wadann
mutane ba'a zauna haka kawai dasu dole ka
nemi tsarin kanka sabd zasu iya halaka mutum
tinda ba I mani a zuciyoyinsu,
Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours ago
Pharidah Ahmad
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 9鈨�0鈨�
amma gud karki yarda araina ki har mijin ki
cigaba da bin hakkinki agunsu, amma pa bance
kiyiwa manaya rashin kunya ba kokuma mijinki
agabansu kinuna masoyinki ne " se kun kebe
sann kibasar tinda bashi yake bukatar zamanku
ba karki taba nuna masa kindamu dashi hakan
zaisa yayi kishin ki har yanemi baki mazauni
agidan sa, joda tasauke ajiyar zuciya sann tace
wlh mama bana sansa kallonsa ma dakyar nakeyi
natsanesa tamkar yanda natsani mutuwa na
Mama tace subhanallah joda mijin naki gara tin
wuri kikoyawa zuciyarki sonsa danko bana Jin
aurenki akwai saki aciki koba komai ga zumuncin
ku , kezaki gyara masa zama tinda yafara low
yanxu kiyita yi masa tsiya kina zuba shagwaba
dama ke gwana ce gurin shagwaba , joda tace
toh mama zan gwada Allah yashige mana gaba
ameen "
khalthum tajata sukayi daki, suna kara waye kan
junansu, joda tace kinsan Allah khalthum yanxu
wann doctor din nake bala'in so, komai nasa
daban ne dana sauran maza ya iya soyy kamar
me, khalthum tace garama kicirewa zuciyar ki
sonsa kimaida shi ga Ahmed yafi miki sauki, joda
tace uhm....abar zancen kawai bazaki gane bane
Bata dawo gida ba se bayan magrib atare suka
dawo da khalthum sann driver din joda yamaidata
gida, bayan kh tawuce tayi wanka tasaka
nightwear sann takwanta, Ahmed kuwa duk
hankalinsa na gun joda yana tunanin yanda zaiyi
da ita, wann renen datake ji, tabbas turo ta akayi
tayi masa wann iskancin amma yasan maganinta,
mansura tayi bacci tazo takwanta kusaga
Ahmed baice mata komai ba, a hankali tace dear
please inason canjin mota kuma inason kudi
nasiye gwala gwalai Ahmed yace banganki da
kodaya ba naci kin lefenki zaki ce nabaki kudi
kisiye wasu, mansura tace shikenan , kasiyawa
joda mota ka kaita wani gun angyarata nikuma
nice banza, Ahmed yace bansan komai a kanta
ba gadon ubanta ne take amfani dashi,
mansura tace amma dai kafara santa tinda har
take iya daga maka hannu agaban kawarka
kamata banxa , Ahmed yace yafusata yace wai
ke bakida hankali ne " yarinyar da kuruciya keci
idan nabiye mata ayseta re nani, mansura tace to
meyasa ka kwana adakin kamar yanda tace
Ahmad yaballah mata harara ubanwa yagaya miki
cewa agidan na kwana ma bare na kwana daki
daya da ita , mansura tace hava dae naxata ay
can ka kwana , Ahmed yace ehh akanta ma
nakwana da iskanci ,
zatayi mgn yadaga mata hannu dallah kije kinxo
kin dameni da surutun tsiya, mansura tace
tokabani kudin, Ahmed yacefaya check yace
gashinan sora ki zare Duka kudin Dan naga ke
baki San miye duniya ba , kudi ne kawai agabanki
tin xuwanki agidann banga kin dauko qur'an kin
karanta ba bare azkar sallar ma bayi ki keba
sekin ga dama, mansura tadafe kai hava Ahmed
sallah fah sekace kafura
Ahmad yace ok karya nakeyi kenan, mansura
tace wlh ina sallah, Ahmed yace ay zaki gane
randa kika isheni wlh dukan tsiya zan miki Dan
kin wuce a miki nasiha ko gargadi kinsan komai
kike take wa yar iskar banxa bace mun dagani
kafun in sharara miki mari dasauri tabar masa
parlor din
Ahmed yace gaida dad gidansu sun gaisa yadanci
breakfast. nan dad ke masa zancen joda, Ahmed
yace tunani na kenan dad amma nafison takara
hankali yarinya akwai kuruciya acikinta, dad yace
shikenan har kullum dae ina kara jadda maka
cewa kayi adalci kuma kasa ido akan matarka,
Ahmed yace karka damu dad komai dae2 yake
tafiya, dad yace gud son Allah yamaka albarka
yatabbar da farin ciki arayuwarka Allah yajikan
mahaifiyarka Ahmed yace ameen
A garden ya hadu da joda tana sanye da rigar
bacci duk ta lafe a jikinta , yayan hafsa yaji
tafada yatsaya cak batareda yajuyo ba, joda taci
gabansa, tana marmada ido " ay baka bani kudin
girkina ba kuma ni har yanxu banyi breakfast ba
yunwa nakeji, Ahmed yace to ubanme kike har
yanxu baki karya ba joda tace badai ubana ba,
Ahmed yace to senawa? Joda tace kila naka,
Ahmed yajanyota dasauri ta rufe ido tana jiran
saukar mari sekuma taji shiru tana bude idonta
yana turata gefe , joda tace nifa abuncin gidann
baya mun sann baxan iya girkawa ba dole ka
girka mun kokuma kabani kudi asiyimun, Ahmed
yace zan ballaki wlh kinga namiki kama da mai
girki ne.............
( karfa kuga nayi jiya nayi yau kusa ran zanyi
gobe, a'a tym ne kawai nasamu nayi gobe ma
idan ina free zanyi idan kuma banyi ba toh "
hannuna nason hutu,
Love you all my fans much love
Muje zuwa
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/29/16, 12:14 AM - Queen Safiyyert馃憫: FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 9鈨�1鈨�
Joda tace oho dai ay cina da shana duk a kanka
yake sena gadama zan tausaya maka in dafa if
not kuma either ka girka mun kokuma kasiyomun,
Ahmed yace gud kinyi gsky niba jahila bane ,
abunda kika saba ci gidanku shi zanbaki idan
naso xan kara daga hakan , so zan kawo miki
buhun tsaba da dawa, joda tace kambu yaushe
rabon tsohuwa da sukuwa a gado, Ahmed yadafe
bakinsa dariyar da tazo masa, joda tace kodai
zuwa na gidanga yanxu shekara nawa soni
namanta dawani abu dawa kayan dadi nakeso
Ahmed yazaro kudi a aljihunsa yabata joda tace
da dai yafi maka kuma yau kwana nane dole ka
kwana agidann, Ahmed yace kee wlh nakusa
karyaki, da aurena zandawo kwana agida , joda
tace oh dai wann yarage naka, Ahmed yakwada
mata wayarshi atake ta bare baki, yace idan
kwana kikeso tare dani Dan naga alamar namiji
kike bukata seki sameni agidana, joda tace iyeee
namiji Allah sauwake na name namiji koma ina
neman maza bakaiba se wanda suka amsa sunan
su na maxa ,
Ahmed yafusata yacakumo wuyanta yabata mari
biyu kyawawa , kidena ganin ansamiki ido kizata
tsoronki ake wlh zan gyara miki zama niba sa'an
wasanki neba, ubanme ma zai kaini hada jiki
dake, joda cikin muryar kuka tace nadaifi
tsohuwar matar ka da kuka kusan zuwa age daya
kuma ka duba dakyau har abada baxaka samu ko
maikama da joda ba bare joda, Ahmed yabita,
aykuwa tace kafa minaci ban bakiba se dakinsu
aguje tafada kan gwaggo tana maida nunfashi
Kusan 5 millions mansura taxara a account din
Ahmed ta turasu anata , haka take kwasar kayan
abincinsa tana aykawa kasuwa ana seda mata,
hjy kuwa itama tazage dantse tana kwakwulal
aljihun dad, se abunda ya gagareta, amina ma
haka take ta tsan Mahmud shikuwa bai gane
komai, gwaggo tagama fura tabawa joda ta
kaiwa dad, joda tasaka karamun hijab taje har
kofar tayi Knockin akabata izinin shiga , fridge
takai masa furar sann taxo suka gaisa dad
yamata nasiha sosae akan mijinta da rayuwar ta
Joda kwance dakin Ahmed kan gado tayi rufa da
blanket, tana wasa sa flowers din bedsheet din
dae2 nan Ahmed ya fito wanka Wanda baisan
shigowarta ba itama kuwa batasan yana gidan
ba, lafewa tayi kamar bata agurin tana kallonsa,
key yasakawa kofar sann yadawo shiri joda na
ganin ya cire towel tabuga ihu sedai bakinta
adafe ba'a jinta, rude idonta tayi gam jikinta se
bari yake , Ahmed kuwa boxer dinshi yasaka se
vest yafeshe jikin shi da turaruka kala2 mouth
spray yafesa sann ya kashe light, joda tazaro ido
yau na banu na kawo kaina
Ahmed yafada kan gadon aykuwa joda tasaka
kara seda yaji tsoro yakoma baya dasauri ,
yanunata da yatsa yace you! mekikeyi adakina
yaushe ma kika shigo bayan nasaka key ? Joda
tace yo ni ay banma San kana ciki ba se gani
nayi kafito agurin wanka, Ahmed yazaro ido
what? kina nufin koda nafito toilet kina nan, joda
tace ehh mana, naganka ma. Ahmed yace kinga
me? Joda tace naganka ba kaya kato kato dakai ,
Ahmed yace kallona kikayi ina shiri yadafe kai
ohh...gosh wann yarinyar tagama dashi Ahmed
yace shine baki rufe ido ba koh? Joda tace
oh..dai yaudae naga komai bawani dae2 dazaka
sake mun naga ciki naga waje joda ana tsula
tsiya wollah
Ahmed yace kuttt wlh yau sekin gane, joda
tace mezan gane nadai ganka ciki da baya,
Ahmed yarasa mezai yi, yadafe kai, sann yace
kema wlh sena miki tsirara, joda tace wayyo ni
Allah nah wayyo gwaggo wlh ban ganka ba kana
zare towel na rufe ido yaushe idona ya isa
daukar halittar namiji katoto dashi , Ahmed
yadanne dariya yace ohhh...zama ki fadi gsky ,
wato karya kika mun, joda tayi shiru, can kuma
tace nidae budemun daki in fita Ahmed yace
wann kuma baki isaba........
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 9鈨�2鈨�
Joda tashiga bubbuga kafa ni wlh kabudemun
kokuma namaka ihu " Ahmed yazagaya baya
yahau gado yayi rufa yabarta agurin tanata mgn
ita kaday, can tajishi shiru ta yaye bargon taga
ashe har yayi baccin sa, joda tace toni ma ay
baccin nakeji bara na sauka kasa, pillow tajanyo
da bargo tashinfida kasa tayi kwanciya ta , hadari
ne yafara haduwa iska da kura suka taso,
abubuwan dakin suka fara rawa joda tabude ido
taga duhu yakaru gakuma abubuwa na rawa,
aykuwa ta takure guri guda
Can plate yafado akan table dasauri joda tabuga
tsalle tafada kan gado se ajikin Ahmed, Ahmed
yace ke ke lfy? Joda tace wayyo ni yayan hafsa
ka kaini inda gwaggo na aljanu suka shigo
dakinka , Ahmed yace ke dakata mun dallah
ruwa ne ke zuwa, joda tarike shi gam a'a nidae
yayan hafsa, dakyar yabanbare ta yaje yarufe
windows,
wani kyalle yafado mata aykuwa anan tadaka
tsalle se gurin sa, tarike shi , Ahmed yace kewai
bakida hankali ne bazaki sakeni ba joda tamasa
banxa sema kara kankame shi tayi, Ahmed
yabuga tsaki yace kisakeni nace kobakya ganin
abunda kika rika joda tadago idonta dasauri
tasakesa taja dabaya Ahmed yagimtse fuska
yakoma kan gado yayi kwanciyarshi
Joda kuwa tabisa Ahmed yace ke kikuma kasa
kokuma ubanwa zai kwanta dake guri guda, joda
tace al qur'an ba inda zani sokake a wurgo mun
wuka, Ahmed yace toh shikenan, joda kam gado
tahaye tayi kwanciyarta, ba'a Fi minti uku ba
bacci yayi a won gaba da ita , Ahmed yarufa
mata bargon shikuma yajuya baya,
can cikin bacci ko mafarki tayi kome
oho....kawai ji yayi yarikesa gam tana kuka,
Ahmed yajuyo da nufin zai bigemata hannu seya
ga hawaye a fuskarta idonta rufe bakinta na
motsi, a hankali yakai kunnensa gurin bakinsa ,
mezaiji tana fada....,
yayan hafsa ka cuceni ka wulakanta ni kanuna
mun kiyayyar badan taba ganiba , bazan taba
yafe maka Allah zai kamaka da cin zalun dina
hakama maraicina baxan yafe maka ba baxan
yafe maka ba......Ahmed yasaka hannunsa yarufe
mata baki aykuwa tasa kuka Dan Allah kada
kadokeni, Ahmed yace kee keee, dasauri tabude
idonta, Ahmed yace mekikecewa ne acikin barci
mafarkin wa kikayi ?
Joda tayi shiru ba tace masa komai ba se
hawaye take, Ahmed yayi shiru aransa yace
dama haka yarinyar nan tarikesa yaxamemata
dodo har mafarki na take zanci zalun ta. lallae
dole nabi mata wata hanyar da zata ya femun
danko baxan iya neman gafarar taba, hakan zai
kara sakawa tarainani, akan na yanxu , joda tace
idan angama ruwa kabudemun daki inje inda
gwaggo na,
Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours ago
Pharidah Ahmad
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 9鈨�4鈨�
Ahmed yace ba'a gamaba bakya jinsu ne " wata
tsawa aka daka joda tayi bala'in rikesa tana kuka,
Ahmed yace lfy kewai komai kuka, joda tace
yayan hafsa wlh bana sanka banason kallon ka
amatsayin mijina Dan Allah kabani takardarta
inada masoya, Ahmed yace nikuma maqiyinki
koh?
Joda tace koma dai yane nidae nagaya maka wlh
bana son ka bana son ka, Ahmed yace shikenan
naji zan baki takardarki amma sekin yafe mun
Joda tace kambuu ay wlh sedai in tabbata da
aurenka aka ina mara amfani amma baxan taba
yafe makava,
Ahmed yace auren ne mara amfani? Joda tace
eh mana miye amfanin hada makiya guri guda,
Ahmed yace toh naji ya isa haka, me kikeso
inmiki seki ya femun joda tace babu shi, Ahmed
yace idan nace zan baki takardarki fah Joda
tajuyo da murmushi har dimple dinta ya lotsa
dagaske zaka bani takardarta,
Ahmed yace of course idan kinbi tsarina, joda
tace me kenan , Ahmed yace zaki koma gida na
ma'ana ki karbi aurenki na tsawon wata biyar
nikuma namiki al_qawari suna cika xan baki
takardarki , joda tace shikenan na yarda, Ahmed
yace kuma baxakimun fitsara ba komai nace dole
kiyi, joda tace na yarda, kaikuma idan ka cuceni
Allah baxai barkaba, Ahmed yace naji, doka
tafara daga yanxu,
Tashi kihadamun ruwan wanka, joda kamm nifa
bansaba da aykin wahala ba, Ahmed yace lallae
yarinyar nan mijinki fah, joda tace wai mijina ,
mijin mansura dai Ahmed yace au zaki saba doka
kenan, joda tace shikenan ina ne toilet din Ahmed
yanuna mata tashiga ciki seda tafara wankewa
sann tahada masa ruwan, bayan tafito tace masa
gasu can ,
waima bayanxu kafito ba daga wanka ba, Ahmed
yace ehh ay wann ma kece sila, joda tace
nikuma kamar ya? Ahmed yace manta kawai
sena fito kifidda mun kayan sa zansaka, joda
tace kai wlh baxan iyaba dama haka ne auren
komai se anma miji
Ahmed yace bakya son lada kenan Joda tace
inaso mana , yana shiga seta gyara gadon tsab
tagyara dakin ta kunna tirare bayan tagama
tajanyo wadrop dinshi tafidda masa wando 3Q,
da riga tafashesu da turare,
Ahmed nafitowa joda tajuya bayanta, yace no fah
ay baki gamaba zoki gogemun jikina ki shafa
mun mai, sann kisaka mun kaya, joda tace
kai_ka_kai sekace wani jinjiri, Ahmed yace yo ay
miji jinjiri ne idan yana agaban matarshi kuma
kince zakiyi duk abunda nasaki joda tace ni wlh
tsoro nakeji bana iya saka maka kaya , Ahmed
yace shikenan wasa nake zo kiyi alwala kiyi
sallah kinga 4:20, ba musu tashiga toilet din tayi
alwala ta tada sallah
Bayan tagama Ahmed yace zo nan joda zan
tambayeki, joda tazo tazauna Ahmed ya kamo
hannunta yace gaya min meya sameki abaya
bayannan naga kinyi wani iri kina zama da datti,
joda tafara kuka, Ahmed yace ba fah kuka
nakeso ba kigayamun naji, joda tafara basa
labarin komai bata boye masaba, ran Ahmed
yabaci matuka idonsa sukayi jajir
hannunsa nadama yafara rawa joda kam ta
tsorata dashi, baya baya tadinga yi karya
nausheta, se wani gurnani yake like a lion. Joda
tabisa a hankali takamo hannunsa tahada danata
ta rike gam sann tafara shafa bayanshi a hankali
ya lumshe ido yakwanta kan kafafunta, joda ta
cigaba da shafa masa kansa , sunfi minti goma
ahaka sann tada gashi taje fridge tadauko masa
eviron drink tazuba masa bamu su yakarba ya
shanye Tass
Yana gamawa yakirata joda zo naga jikinki, Dan
kwalinta yacire yana taba gashinta yaga ma
kamar yafi da tsawo sann yafi jikinta da kallo
bawata matsala, yace meyasa baki gayawa kowa
ba, joda tace sunce zasu ballani idan nagaya wa
wani sekuma tafashe da kuka, Ahmed yarungume
ta yana shafa bayanta it's ok kinji..............
Muje zuwa
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours ago
Pharidah Ahmad
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 9鈨�5鈨�
Ahmed yaje yaga dad yamasa magana kan cewa
ran Friday joda zata tare gidanta baya bukatar
komai shi zaizo yadauki abunshi da dare, dad
yayi matukar murna dajin hakan, shima yaje
yasamu gwaggo yamata bayani, itama din murna
tayi sosae daga ranar aka shiga gyaran joda ana
tirka mata kayan fruits, hjybinta kuwa gyaran jiki
take mata kafun kwana shidan suzo sekunga
yanda joda tadawo abun sewanda yagani skin
dinta kamar zai fashe idan kataba
Joda tasamu khalthum tayi mata bayani,
khalthum tace aykuwa yafi ma seki kara wanasa
, khalthum a ranta tace lallae joda bakida wayo
kafun 5 month din yakoya miki yanda zaki soshi ,
ni hakan ma yayi mun ina sonki da, Ahmed kodan
ki gyara masa zama kamar yanda kika gyarawa
abdallah nasa
Angama hada komai tsaf dad yakira joda yayi
mata nasiha kamar haka , joda ina son kirekemun
dana amana kamar yanda nabasa umarnin yarike
ki amana nagayama sa tabbas idan yacuceki
tokuwa ban yafe masa ba , inaso kiyi amfani da
iliminki da tarbiyar dakika samu kigyaramun wasu
halaye na Ahmed, tinda kika gyara abdallah
Ahmed baxai miki wuya ba , ki daure kiyi ibadar
aure kisamu aljanna iyayenki ma zasu samu
Banda fitsara da shashanci dukda nasan wann
bahalin ki bane idan kika iya Ahmed bayada
wuyar zama, ki kama kanki daga matarsa karki
shiga lamuranta inso samu ma kada ki hada
hanya da ita seta kama dole , allah yabaku
zaman lfy da zuri'a dayyaba ameen " dakyar aka
banbare joda daga jikin gwaggo, ita kuka gwaggo
hawaye, gwaggo takasa mata wata nasiha kawai
tace mata Allah yabaku zaman lfy yakauda
shedan azamanku ameen
Tin da Ahmed yatada mota takara wani ihu kuka
take kamar me, Ahmed baice da ita komai ba,
har suka kai gidan yafito itakuma taki fitowa
zagayowa yayi , yabude ganbu yajawo hannunta
sukayi cikin gidan , kwance take kan kafadarsa
tana kuka har suka kai dakinta yabude mata "
suka shiga yanuna mata komai hadda lefen ta
agurin sak irin na mansura babu banbanci ,
dakinta kam ko makiyin Allah yagani yasan
anhadu se kamshi yake joda tafada kan gado
tacigava da kukanta
Ahmed yace mata shikam seda safe, aykuwa ta
taso dasauri ni kadai zan zauna anan ni wlh tsoro
nakeji, Ahmed yace to sokike in kwana adakinki
koya? Joda tace eh kokuma nabika adakinka,
Ahmed yace yo na banu muje din . dakinshi
sukaje takwanta shi kam toilet yaje yayi wanka
yasauya kaya sann yasha coffee. se yakwanta,
joda na karshe Ahmed na farkon gado haka
sukayi baccin su , anfara kiran asuba Ahmed ya
farka koda yaduba joda tadawo ajikinsa ta lafe
masa kamar mage aransa yace wann yarinyar
kodai mage ce iyakaci kenan wann shegen son
jikin nata
A hankali yasaketa ajikinsa yaje yayi wanka yayi
brush yawuce masallaci yabarta tana bacci, koda
yadawo yasameta kan sallaya tana karatun al
qur'ani, tana juyowa tace ina kwana yayan hafsa,
Ahmed yace lfy lau kn tashi lfy joda tace lau ,
bayan ta ida karatu tace yayan hafsa ina ne
kitchen in hada mana breakfast, Ahmed yace no
an yafe miki kibari se zuwa gaba kadan............
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 9鈨�6鈨�
Su hafsa andawo hutu, taji dadin wann lbrn wai
joda ana gidan Ahmed, gun khalthum taje suka
yo inda joda, Sallama sukayi mansura na falo
tana kallo, kallon banxa tamusu sann ta cigaba
da kallonta, hafsa tace anty mansura ina wuni,
mansura tace yana gidanku daban wuniba da zaki
ganni anan, khalthum taja hannun hafsa sukayi
sama,
mansura tace gidan ubanwa zakuje khalthum
tace gidan uban mai tambaya, mansura tazaburo
dakarfi, hafsa tace Dan Allah anty kiyi hakuri,
khalthum bata sauraretaba tayi ciki, mansura
takoma dakinta tacigava da hutawarta ba sallah
bare salati Ihu joda tadauka ganin su hafsa duk
tarude tama rasa abunda zatayi aykuwa tashiga
jibgo musu abunci pizza da kaji se lemuka,
hafsa tace iye sukike ci ne " joda tace eh wai
baya bari inyi girki ni bantaba sauka kasa ba tin
randa naxo gidann, khalthum tace kenan baku
taba haduwa da fitsararriyar amaryarki ba , joda
tace aifah ina side dina ina Jin motsinta some
time, hafsa tace ay haka yafi, joda tace nifa
inaga bata san da zuwa na gidann ba yanda
nakejin tana waya da karti datasan ina nan dole
tarage wani abu " hafsa tace uhm..allah ya
kyauta
Fira sukasha sosai se kusan mgrb sann suka fito
joda tahada musu kayan make up na cikin lefen
ta. hafsa tace a'a baxamu karba ba, joda tabata
fuska to mezanyi dasu sunmin yawa wlh, dole
suka karba badan sun soba, har gate takaisu
sann tadawo anan taci karo da mansura tarava
ta gefen ta tawuce mansura tadaka
mata tsawa ke ina xua, joda tabuga mata tsaki
sann tayi wuce wata sama, mansura tabita
dasauri wai ina zakije nace basu hafsa sun wuce
ba ke kuma pa meya dawo dake joda tace eh sun
wuce zasu gida nikuma nadawo saga rakiyarsu
na shigo gidan mijina kuma habibiy na, hannu
tadaga zata mareta sega Ahmed yace ke ke lfy?
Mansura tace wann marar kunyar yarinyar mana
wai gidan mijinta, Ahmed yace eh karya tayi ne
nan ba gidan mijinta neba, mansura tace wai
bala'i billahil'azim baxan zauna da ita ba, Ahmed
yatada kafada fine kofar gidan abude take dama
ni kawo ki ne ? Joda tace kuma kadaya mata
tabini sau dakafa Dan nice uwar gida nice babba
bazan cen shekaru
Ahmed yaje famata key din mota dake nake
magana, joda ta bare baki wlh ban yafe ba,
Ahmed yabita dasauri ta rufe ganbun dakin
dakarfi, mansura tajuya afusace tahada kayan ta
tafito taja mota tabar gidan, Ahmed na kallon ta
yamata banxa gidan su taje tazayyane wa uwarta
komai, innasarsu tace to miye aciki tinda
bakulata yakeba
na tabbatar ubansa ne yace dole yamaida ta
gidanshi kedai kawai kikoma ki cigaba da ya go
mana shi, dahaka aka batar mata da kishin ta.
zuwa 11:30 tadawo gidan, shiryawa tayi cikin
kayan bacci taje dakin Ahmed ko kallonta baiyiba
taduka tabasa hakuri , Ahmed yace shikenan
yawuce daga nan suka lula wata d
9/29/16, 12:24 AM - Queen Safiyyert馃憫: FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 9鈨�7鈨�
Tin randa joda tazo mansura take samun biyan
bukatar ta agurin Ahmed har se ta ki wani
lokacin, dalili kuwa joda ce keruda shi amma
tsabar jinkai da karta renasa yasaka yake neman
mansura dukda tana gamsar dashi 70% amma ko
kadan ba itaba sha'awar taba , mansura kuwa
ansamu yanda ake so har anfara wani epixy
epixy ,
joda kuwa al amarinta take baruwanta da kowa
agidan barinma yanda taga Ahmed ya share ta.
itakuma tafita har kanshi ko mrng tadena yimasa,
se hadu tarava masa hanya amma bawanda zero
yiwa wani mgn Kullum safiya seta zana da biro
kwana Kin da tayi agidan , yau Watanta biyu cif,
joda takara cika yanda take cin kayan dadi
gakuma hutu aykin komai batayi se gyaran
dakinta, yau tashirya cikin wata atampa brown
tayi kyau, tanada dankwalin ta simple taje dakin
Ahmed tareda mansura tasamesu suna iskanci
inji joda aranta tace tanbadaddu kawai se ayita
ta shafe2 iskanci , baya tabasu sann tace ina
son zuwa gida inga gwaggo na, Ahmed yamata
banza, mansura tace honey ana mgn fah kayi
shiru, Ahmed yace ni Dan iska ne dazan amsa
mata mgn tabani baya
Joda tace nima kuma ba yar iska ceba dazan
kalleku kuna tanbadodi , Ahmed yaxubura
mansura tarikesa yi hakuri cweet heart, Ahmed
yace sekin dawo out kuma daga dakina joda tace
koma baka ceba , ba tsayawa zanyi ba kallon
iskanci, allah yashirya wanda yabata tana kai nan
tawuce, Ahmed yayi tsaki sena karya wann
yarinyar watarana
Zuwa aza har tagama shirinta tsab ta rufe
dakinta tadauko kasa, mansura tace har kin fito,
kigaidasu Allah kiyaye joda ta yatsina fuska
ameen idan dagaske kike, Ahmed yace kewai
bakida hankali koh se kiyi ta yiwa manya fitsara,
joda tamasa kallon banxa tawuce abunta,
mansura amma dae honey baida ce kabar ta taje
gida ita kadai ba zuwan fari kuma ni banga tayi
wani tsara ba ba hannu rabbana zataje, Ahmed
yace hakane ina zuwa, ciki yakoma yasauya
kayan shi sann yabita dae2 gate yayi wa maigadi
hannu alamar kar yabude gate.
Ahmed yasameta yace mata kee fito muje
amotana , joda tace why bayan gatawa, Ahmed
yace to haka nakeso, joda tace nikuma bahaka
nakeso ba , Ahmed yace zan ballaki fah ki fito
kafun na saba miki Joda tace ni banida
hannuwan tuka mota ne se anjani, Ahmed yace
shikenan karki fito wlh ba inda zakije, joda tace
so what? Fitowa tayi a motar tarufe ganbun da
karfi tabuga masa dogon tsaki sann tawuce ciki,
Ahmed yabita da kallo
Hafsa tafito zata inda gwaggo ana tahadu da
Mahmud, yana waya da amina dae2 kunnenta taji
yace I love you amina more than you could think
" wani kololo taji yana taso mata a zuciya zafi
zuciyar keyi aykuwa tadafe ta anan tafadi timm,
Mahmud yajuyo yayi kadi da wayar yace hafsa
koda yadago ta jini abakinta dakyar ta iya furta
ya Mahmud kawai seta yi baya , wayarshi yaciro
yakira Ahmed, Ahmed baijira yagama bayani ba
ya tsinke wayar, motarshi yafiga yazo gidan Allah
ne kaday yakaishi lfy
Basu tsaya wata mgn ba, aka wuce asibity da ita,
duk atare suka shiga, Ahmed da Mahmud
dasauran likitoci dakyar aka shawo kanta jininta
ne yahau sosae ga dunbin damuwa yamata yawa,
Ahmed yace wai menene silar wann abun ne "
anan Mahmud yagaya masa yace nikam ina waya
da amina kawai se jinta nayi akasa tafadi amma
ko menene zai saka mata damuwa haka har ta
haifar mata da hawan jini , Ahmed yace shut up
Mahmud b4 I kill you, kasan komai duk ciyon 6ter
a kankane kokuma kanaso kace mun bakasan
tana dauke da cutar sonka ba , yarinya na neman
mutuwa a kanka taboye sbd kunya da kawaici
kasani baxan taba yafe maka ba idan ta mutu a
kanka sann kotu ce zata rabamu, dae2 nan
tafarka da tari.........
Muje zuwa
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours ago
Pharidah Ahmad
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 9鈨�8鈨�
Dasauri Ahmed yaje gurinta yarungume ta yana
shafa bayanta sannu 6ter kinji, hafsa tashige
ajikinsa taki kallon Mahmud, shikuma jikinsa yayi
sanyi, a hankali tace ya ina son ganin joda na,
Ahmed yace mezatayi miki anan, hafsa tace
nidae kawai joda nake son gani, Ahmed a'a
bayanxu ba kibari har ki kara samun sauki , shiru
tayi Dan bata san musu sekuma tadinga kuka,
Ahmed oh god wai mezata miki ne iye
Mahmud yace joda kika gani? Tagirgixa masa kai,
wayarshi yaciro yasaka Kiran joda, tana dagawa
yace mata kizo hafsa batada lfy tana asibity ke
takeson gani, baikarasa ba ta tsinke wayar hijab
kawae tasaka tarufe dakinta tafigi mota aguje se
asibity, tana xuwa tayi tambaya aka nuna mata
dakin da suke, Sallama tayi sann tashiga daga
ciki, dasauri tayi bayan hafsa tana meyasa meki
hafsa na
Hafsa tace bruhh zamuyi mgn plss " Ahmed yace
no hafsa zata tsira mana koke koke anan,
Mahmud yace mubasu gurin Ahmed dole suka
fita, Ahmed yace karki manta bai dace kiyi
doguwar mgn ba kokuma ki tada hankalin ki
kinsan dae condition dinda kike ciki , hafsa tace
tou bruhh, hannun joda tarike tace plss joda karki
bawa kowa labarin wann buk din plss, joda tace
hafsa so kike ki kashe kanki da kanki, yazaki ta
boye so azuciyarki yana neman kai ki lfr kisani
idan kika mutu kece kika kashe kanki da kanki,
hafsa tace ay dama akan hanyar mutuwa nake
Joda tace ni bazan bari ki mutu ba, hafsa tace
joda kada ki fallasa sirrin buk dina har se bayan
raina, daga nan tafara tari jini yana fita Da gudu
joda tafito dakin tana kuka Ahmed da Mahmud
suka bita da kallo Ahmed yadan bi bayanta, mota
tabude tadauko wani littafi, tazo dae2 gurin
Mahmud tajefamasa, ya Mahmud ka karanta kaji
, komai yashafe hafsa na wlh kaine Mahmud
yaduka yadauki littafin yana budewa yana
karantawa har karshe, joda tace u see koh "
wuyanshi ta cakumo tana jijjigashi wlh idan ka
kashe mun hafsa na baxan taba yafe maka ba
Kuka take sosae, Ahmed yaxo yajanyota ya
rungume ta ajikinsa yana bata mgn, joda kiyi
shiru hafsa bazata mutu ba seta auri Mahmud
sun haifa babies. dasauri joda tadago tace Dan
Allah yayan hafsa da Dan murmushin ta, Ahmed
yace eh , cike da Jin dadi, joda tarungumesa,
harda basa kiss a cheek wanda yasaka Ahmed
susu cewa, duk lokacin da yahada jiki da joda se
hakan tafaru, wani abu yakeji baisan ma koya
neba
Mahmud kuwa dakin yashiga dasauri yadago
hafsa yagoge mata bakinta sann yabata ruwa ta
sha, Mahmud yace hafsa meyasa kika boye mun
soyyr ki har kika bari nafara son joda by den
kuma yayarki, hafsa shiru tayi ba tace komai ba,
Mahmud yarungume ta, I love you hafsa I love
you so much. dasauri ta banbare jikinta anasa ya
abunda kake fada har zuciya yake kome?
Mahmud yace wlh 4rm d bottom of my heart ne "
Ahmed ne baya son yaga ina nuna zake wata a
kanki shi isa na boye sonki araina haduwa da
joda sonki ya narke mun, rashin samun ki yasaka
na nemi amina dukda kamarka afuska ne
halayenki basa kama da Juna , hafsa takara
rungumesa ilove you more than you think.
Mahmud yace it's ok love you too. Okey " haka
suka dade suna fa ranta ran Juna Mahmud
nacigaba da lallashinta har bacci ya kwasheta.......
9/29/16, 12:27 AM - Queen Safiyyert馃憫: FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 9鈨�9鈨�
Ahmed yadago joda yagan har tayi bacci,
murmushi yayi wann yarinyar kamar jinjira take
daka sakata ajikinka yanxun zata maka bacci,
Mahmud yakira awaya yace masa zai maida joda
gida tayi bacci, Mahmud yace hava kae joda
akwai son jiki
Mahmud yace kana fama fah, Ahmed to yazanyi
yarinyar ce se a slow yanxun natada ita tasaka
mun kuka , Mahmud yace c Ahmed woooo, kaine
yau kake gudun kukan joda da , lallae so baiyi ba,
Ahmed yace bansan iskanci fah kanwata ce fah
ko ka manta ne " Mahmud yace no I remember.
amma ay ada din da kake cutarta kasan kawarka
ce yanxun dae kagan ta waye kuma ta iya fitsara
shine kake zaka matmata halin maxa na yaudara
ka koya mata sanka koh? Ahmed yace kaifa Dan
iska ne so ya eh . kai kasan wann kalmar kuma
kaika ke amfani da ita, Mahmud yace naji dae na
joda
Tsaki yaja ya tsinke wayar tadauketa cak se a
mota, har yakai gida ko motsi batayiba, hakama
nan yadagata cak se dakinta ya shimfideta kan
gado sann ya juya, dakinsa yaje yakwanta har
yafara bacci kawai seya farka yana son shan
lemu, murmushi yayi ganin mansura har ta ajiye
masa Lemun kan table wanda yake sha idan
yadawo daga ayki
Dauko sa yayi ya shanye Tass aransa yace tasan
abunda nakeso wato yau zata fita shine takawo
mun kar na duba babu raina yabaci, mtsw yaja
tsaki zan koyi sonta"! Tass ya shanye yakoma
kan gado amma me wani iri yakeji yama rasa
menene wann yanayin wayarshi yaciro yasa kiran
mansura amma taki dagawa
Mansura kuwa ana can gurin boka ana aykata
masha'a, daya ga dae abun bana Kare wa bane
dole yashiga toilet ta watsa ruwa, amma kamar
abun karuwa yake mace yake bukata kowace iri
ce, marar shi ce tafara murda Ahmed se cije
lebe yake duk yanda yaso yadaure amma yakasa
yanda gumi ke karyo masa gakuma jikinshi
dayake bari sewani jiri yakeji
Joda ce tafado masa arai " a daddafe yakai kofar
dakinta rike da ciki, yamurda kofar dakin yaci
sa'a kuwa tabude ganbun, dakyar yasamu
yashiga ciki , dae2 nan joda tafito wanka daure
da towel. ihu tasaka ganin Ahmed a dakinta
ayanda take " dasauri tajawo hijib tasaka ' se a
lokacin talura da halin dayake ciki , dasauri tayo
gurin sa tana yayan hafsa meyasa meka lfy
kuwa? Ahmed yakasa amsa mata sema wani
kallonta yake gumi nata keto masa , wani kara
yayi sakamakon murdawar da marar sa tayi, joda
kam tini tasaka kuka wayyo Allah na yayan hafsa
Allah yasa dae ba mutuwa xakayi ba kabarni plss
yayan hafsa I beg.
Ahmed yace yajawo ta yarada mata a kunne,
plss joda help me mutuwa zanyi, joda takara bare
baki wlh baxaka mutuba yayan hafsa ina nan
tare dakai, Ahmed yace help joda help plss ohhh
god, joda tace wani iri taimakon kake so, dakyar
ya iya furta joda I need you koba keba kowace
mace inada bukata yanxu yanxu
Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours ago
Pharidah Ahmad
FULANINDAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�0鈨�
joda tace dafe kai tadinga yi baya2 tana
girgiza kai baxan iyaba yayan hafsa baxan iyaba
" so kake kara bani da mutunci na, never....,
ganin tayi Ahmed kansa takai kasa dasauri
tadawo ta cakumesa dakyar ta do rasa kan gado
tana masa ferfita dukda ga sanyin AC adakin ,
Ahmed yalumshe ido tamkar yayi bacci joda
kuwa ta tafi wata duniyar, hijabinta yacire ,
afirgice joda tajuyo tafara kuka Ahmed kuwa
idonsa yarufe ya walwale towel din
Kiss romance ba abunda baya mata kuka take
tana turesa amma ina baya ma jinta nikam
tausayi ya hanani tsayawa dole nafito, sunfi
karfin awa uku sann yabarta shikanshi ya wahala,
rungume yake da ita bata koda motsi bare tari ,
sunkai 30mnt sann ya daure yatashi a toilet dinta
yayi wanka yaje dakinshi yasaka jallabiya sann
yadawo yahada mata ruwan zafi da dettol,
dagota yayi cak se abawon wanka kara tasaki ta
kankame shi sosae Ahmed yace yihakuri zaki
samu relief dakyar takai 8mnt aciki Ahmed
yahada mata ruwan wanka yafito yabata guri,
kafun tafito har yacanza bedsheet ya kunna
tirare
Kayan bacci ya fidda mata shine yataimaka mata
tasaka, a hankali tafada kanshi Ahmed yajata a
gado ya kwantarda ita, sann yahada mata tea
mai kauri, dakyar tasha kadan. sann yakoma
dakinshi yadauko mata magani seda yafara mata
fada sann tasha maganin , shikanshi seda yasha
sann yabita agado ya rungume ta yana tancuu
kanwata kinkawo yancinki agidan mijinki nagode
miki Allah yayi miki baiwa sosee wanda baki
baxai furta taba ,
Allah yamiki albarka, joda najinsa tamasa banxa
jitake bawanda ta tsana aduniya Sama da shi,
kuka take ciki2 har bacci yakwasheta shima din
baccin yayi, se wani lokacin suka farka atare
joda takasa hada ido dashi se wani kasa dakai
take Ahmed yabar dakin ta yakoma nasa " dakyar
ta tashi tayi sallah tahada lipton tasha sekuma
takoma bacci tsantsar bakin ciki dayake damunta
idan ta tuna abunda Ahmed yamata harma
takasa kuka
Ahmed kuwa jinshi yake tamkar me tsabar farin
ciki, daga ranar bata sake bari sun hadu da
Ahmed ba, shima haka ita tana cike da tsanarsa
gamida kunyarsa shikuma yana gudun tamasa
kallon raini, Mahmud ne suna waya da amina
take gaya mas cewa ya hakura kawai ya nemi
wata itakam Dan gov garin zata aura , Mahmud
yayi murmushi dama yana tunanin yanda zai
bullo mata, se bainuna mata komai ba, kawai
yasamu iyeyensa aka je nema masa hafsa wadda
xuwa yanxu takoma garau, aykuwa tasha arashi
da habaici akan cewa amina tayi yayin Mahmud
tagama sann tabar mata " jifa sekace wani
atampa
Aykuwa dad yayi matukar murna hakama gwaggo
wadda yanxu taxamo uwar hafsa, akasa biki
wata daya, shiri suke kamar me, hafsa da
khalthum da joda , duk yawon datake bata neman
izinin Ahmed danko yafita harkanta aranta take
cewa yasamu biyan bukatar shi ay dole ya
maidani shara, koma dae yane nakusa cika
watannina agidan, mansura kuwa se abunda
tacigava kullum Ahmed yafita seta kira wata
kawarta siddiqa wadda take asalin namiji ne yake
shigar mata suna iskanci su
Yaune za'a fara bikin hafsa, gashi kuma joda
antashi da ciyon zuciya ga yawan zuvadda yawu
sekuma jiri datake ji, haka dae take daure wa
tana shiga mutane, salad suke gyara akace mata
Ahmed yana nemanta aykuwa gabanta yashiga
dukan uku2 danko kwanta uku agidan batareda
tasanadda shiba, tana xuwa tace gani, Ahmed
yace wato ke ko......baikarasa ba yayi shiru
ganin tana dade hanci tana masa alamar
yamatsa, Ahmed yayi cikinta yacire hannun yace
ke lfy? Joda tace plss kaje bana son wann warin
na tiraren Ahmed yazaro ido yace medame ke
damunki, joda tace jiri kasala....bata karasa ba
tafara kwararo masa amai kamar zata mutu
Ahmed yana ya isa daena kakaroshi,
Joda ta lafe ajikinsa Ahmed yace yarungume ta
yana murmushi...........
Muje zuwa
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours ago
Pharidah Ahmad
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�1鈨�
Dakinshi yaje da ita yakaita toilet yawanke mata
jikinta sann shima yayi wani wankan, akwatinshi
yajawo yabata magani da Dan tea sann takoma
kwance, bayan yayi sallah yadago ta zai mata
magana kawai tafara turashi Dagudu tayi toilet
tana kwara amai, Ahmed yadafe kai ohhh...gosh
wann aman yayi yawa gashi ba taci wani abun
kirki ba
Dole yaje gida yadaukota mata wasu kayan
bayan tayi wanka tasaka su, yana fita itama tayi
dakin Gwaggo kan capet tazube , tana maida
nunfashi, gwaggo tace ke lfy anata ayki kinxo
nan joda tace gwaggo wlh banda lfy bansan
meke damuna ba, gwaggo tace bangane ba
mekike ji, nan tazayyane mata duk yanda takeji
gwaggo tajuya tayi hamdala
sann tace yanxun mekikeso joda tace ni pizza
nakeson ci kokuma Dan wake gwaggo tace ba
damuwa yanxun za'a miki, akwai garinsa agurina,
aykuwa ba dadewa aka gama mata tana Ci Sega
hafsa da khalthum sun zo, hafsa tace ke lfy kike
cin Dan wake da sanyin safiyar nan ga breakfast
can mun hada,
joda tace nikam banson sa wann nakeso,
khalthum tace kaddai babynmu yasamu shiga
musaka lissafi, joda tace kamar ya babaynku
Hafsa tace wayyo dadi I'm gonna be mamma
bajimawa zaki sankado mun baby ammafa boi
nakeso mai kamada yayana,
joda tace wai mekike nufi ne hafsa ta kyalkyale
da dariya, khalthum taje akunnenta tace ya
Ahmed yayi ajiya a jikinki, joda tace lez go to d
strength point mana , khalthum tace ciki ne
dakai, dasauri joda takalli hafsa itama tagyada
mata kai, joda tace billahillazi karya ne anashan
ciki aruwa ne? Khalthum tace oho dai koma yane
dai dubi yanda kika fara fresh dole akwai ciki ,
joda tace tobara kiji ni wlh baitaba kusanta ba ,
kosau daya,
hafsa tace ohhh..kenan maxan banxa kike bi joda
tace hava hafsa yazaki mun wann kalamin, hafsa
tace yo inba maxan banxa kike biba me zaisa
kisamu ciki inba na mijinki bane, aykuwa tuni
joda tafara hawaye to wlh sau daya ne shima wlh
bada son raina ba dakarfin tsiya yamun , aykuwa
su hafsa suka saka dariya harda su bingirewa
zama ki fadi gaskiya inji hafsa , yayana yacika
ayki gwarzon namiji ne yi daya fah wuhuhu
Joda taqulu matuka tayi kadi da tiren Dan wake
tafita Dagudu tana kuka karab sukayi kabra da
Ahmed tafada jikinsa tana kuka, Ahmed yace to
menene kuma joda cikin muryar kuka tace toba
su hafsa neba wai inada ciki, Ahmed yace
ubanwa yagaya musu haka ?Joda tace ohonmusu
, Ahmed yashigo dakin rungume da ita yace wa
hafsa ubanwa yace miki tanada ciki, khalthum
tace yo metake ciwa Dan wake da sanyin safiyar
nan
Ahmed yace zanci uwar yarinya yaxu wlh fever
ce ke damunta, gwaggo tayi dariya to munji
yanxu dae tace pizza takeso Ahmed yace wani
irin pizza bayan taci Dan wake, gwaggo kada a
kara bata Dan wake gaskiya banyarda ana bawa
dana ko "yata wann abun ba, joda tace what
cikin ne dani kenan , khalthum tace au zaka fada
ma...........
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�2鈨�
Ahmed yace no ina nufin idan ansamu, joda tace
billahil'azim se ancire shi ciki dawa zan haihu
aykuwa tafadi akasa tadinga birgima , dasauri
Ahmed ya dagota ke wasa nake miki fah , joda
tace karya kakeyi tasss kakeji gwaggo tawanketa
da mari mara kunyar banza mijinki kike cewa
yana karya saboda bakida mutunci
Joda tafashe da kuka Ahmed yajata sukayi side
dinshi tabaya sukabi saboda mutane suna isa
tafada kan gado wlh wlh seka cire mun cikin nan
kokuma na kashe kaina Ahmed yace bismillah
bansan kincika jahila ba sekin kashe kanki yanxu
yanxu , joda tace ay dai so rana wata daya
agidan ka kasa keni koh? wlh kana sakina zanje
acire mun cikin Dan ba karka shin ikon ka nake
ba lokacin " Ahmed yace kinyi kuskure dakika yi
tunanin zan sakeki da dana ko yata a jikinki kice
kihalaka ta , amma kisani kina juye mun dana tin
agurin zan sakeki Dan bawani amfani kike mun
ba
Joda tace so what? ay haka nakeso amma
kasani da nacika wata na biyar wlh baxan kara
biyarka amatsayin miji ba wai nabi umurninka,
Ahmed yace wann kuma keda ubangijinki " sann
kuma watannin zasu dawo baya, joda tace mugu
azzalimi haka zaka tayin zaluntana har nafi
shekara agidan ka , sekuma tafashe da kuka ni
wlh ban isa haihuwa ba Dan Allah ka duba ni
dagaske cikin ne " Ahmed yace bafa komai
iskanci ne suke miki , joda tace to ay kaima naji
kace danka, Ahmed yace ohh...god ke bari kiji
ciki ne dake kiyi abunda zakiyi faqad
Joda ta dora hannu aka tafashe da kuka macuci
kawai azzalimi.....shiru tayi jin bakinsa anata
seda yatsotse lips dinta tass sann ya kyaleta
yana sakinta tana kuka , aykuwa bakinta baya
mutuwa tace Allah yasa zaka ga annabi mugu
ka.....wani kiss din yadora mata seda
nunfashinta yakusa daukewa sann yasaketa lips
dinta har wani zogi suke akan tsotsa kamar
yakama pop, seda sukayi jajir dasu " Ahmed yace
wann shine hukuncin ki dazaran kin sake mgn
Dole bata kara magana ba , yana fita bacci
yakwasheta koda tafarka har anfara zuwa gurin
party aykuwa agurguje tashiga wanka a toilet din
Ahmed towel tadaura babba sann tasaka karami
akanta tana tsane ruwa , dae2 nan Ahmed
yabude ganbun dasauri takoma toilet gurin rufe
ganbun toilet ne hannunta yamatse aykuwa
tasaka ihu , dasauri
Ahmed yaxo ya riketa yana mata sannu, cikin
fada yace mekike yiwa gudu ne kinje kinji wa
kanki ciyo abanxa, joda kam kuka take barinma
data ga jini nafi ta se wani tsalle2 take Ahmed
yajawo akwatinshi yayi mata dress din gurin
aykuwa ansha kuka da gurje2 duk seda ta cire
towel din nakanta ma seda tacire gurin gurje2
nta gashinta dayake ajike duk yarufe mata fuska
sekuma yabada sexy act! Ahmed yatsaya kallon
ta sann yace mata miye haka zaki mun
tsirara........
Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours ago
Pharidah Ahmad
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�3鈨�
Se a lokacin ta tuna halin datake ciki, aykuwa
tasa lalube takasa da go idonta shikuma Ahmed
dayaga haka kawai seya janye towels din
yamaida su toilet yayi tsaye yana kallon ta, zanin
gado tajanyo tarufe jikinta dashi, Ahmed yatabe
baki sann ya kashe light din yabita agado, joda
taji ana lalubenta dasauri takwabe masa hannu
miye haka? Ahmed yace shhhhh......zo kiji cizo
yabata akunne kadan, tasaka kara nikam fitowa
nayi na basu guri , joda taci kuka kamar ranta
zifita sann Ahmed yasha tsinuwa abakinta,
dakyar tasamu ta tashi tahada ma kanta ruwan
dettol bata raba wann dana fari ba duk zafin
dayane, amma wann karon tafi Ahmed sauki
danko shi yama kasa motsi har tasake wanka
tayi sallah bai daga va, a hankali ta yaye masa
bargon aykuwa rawar dari yake jikinsa yayi zafi
sosae , joda tace subhanallah yayan hafsa meke
damunka, Ahmed yanuna mata akwatinshi na
magani ta dauko masa yanuna mata wanda zata
bude masa, lemu ta tsiyayo masa a cup tabasa
yasha sann tahada masa ruwan wanka dakyar
yasamu yayi wankan yana fitowa joda tahada
musu tea suka sha, zata fita Ahmed yace ina
zua, joda tace gurin party zamuje nama san kowa
yabarni
Ahmed yace jeki shiryo ni zan kai ki , joda tace
no tanks da mota na zanje, Ahmed yace bansan
musu fah kin sani joda tajuya tana ta tunxure
bakinta , takuwa yi sa'a basu tafiba, daganinta
khalthum tasaka ihu ohh maman baby anfito
barayar oga shine kika sharemu ke mai miji ba
koh? Joda tace bansan haka khalthum kidena,
hafsa tace nidai ga kayaki nan kisaka tana karba
zata saka kamshin less din yabuge ta aykuwa
tuni tafara amai, hafsa da khalthum suka rude,
dasauri aka kira gwaggo
Gwaggo tace lfy " khalthum tace daga an bata
anko dinta shine kawai fah inaga bata san warin
sababbin kayan gwaggo tace tabb ke kuma haka
zakiyi mana naki cikin da yawan amai kukira
mijinta, hafsa takira Ahmed tagaya masa yace ay
yana gidan gashi nan zua " koda yazo joda na
kuka tabata kayan ta da amai, khalthum tace yi
hakuri ganawa kisaka amma ina riga batayi Cox
boobs dinta yafara cika, hafsa tace ganata joda
takara fashewa da kuka kayan amarya zansaka
ne? Ahmed yace muga less din yana dubawa
yace to ay tanada irinshi akayanta na lefe
babban wann flower ce kawai banbanci, gwaggo
tace to ay shikenan kuje ta dauko joda tace nifa
bana iya fita yanxu, Ahmed yace nikuma baron ki
bane da zaki ayke ne
Dole badan tasoba tabisa sukaje gidan, dakinta
tabude dakanshi yajawo mata less din ganin irin
kyanshi yasaka ta rungume Ahmed tana tancuu
yayan hafsa, Ahmed yace jimana kirika kulamin
da dana fah naga kina wani rawar kai kinfi uban
kowa tsalle2 da guje2 Allah idan kika sake
abunda ke cikin ki yasamu matsala kema zaki
samu, bakinta ta tabe tacigava da shirinta tsab,
Ahmed yakalleta yace amma kam yau uhn ue kin
danyi kyau kadan, joda tabuga tsaki wlh nadai Fi
matarka kyau, Ahmed yace wakike yiwa tsaki?
Joda tace ahh...wanda yatanka aykuwa taji
unexpected kissa seda takasa daukar kafafunta
Haka bikin hafsa yakasance ma joda bawani
kwarin kirki ajikinta se yawan amai ga jiri, duk
abunn mansura bata saniba, waya suke da hjy
tace kinsan me hjy yanxun haka inada over 20
million a account dina duk ajikin Ahmed suka fito,
hjy tace yauwa ki cigaba da kwakwularsa ,
mansura tace ke pa hjy tace ay nikam ba wasa
yanxun nasaka yacika mun duk wasu kadarori
nasa yanxun haka nasaka masa maganin a tea
na tabbatar yasha, bajimawa zakiji ankira Ahmed
ance yamutu, tuni suka saka shewa, unnnnn
allah ka shirya mu baki dayanmu ameen........
Muje zuwa
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours ago
Pharidah Ahmad
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�4鈨�
Ahmed rungume da joda tagama amai , xua
yanxu ba damar yayi nisa saboda yanda take
yawan amai ga jiri dole koyaushe yana tareda ita,
sekuma me shakuwa tafara shiga tsakanin su,
har idan Ahmed yakai 10 PM bai shigo dakinta
zaka gan joda nata yawo dole se yazo yabata
breakfast , hakama lunch haka dinner , duk
abunda ake mansura bata san wainar da ake to
yawa ba , pizza yake bata tanaci wayarshi tadau
ruri , baiduba ba, bare nasaka ran zai daga wayar
haka wayar tayi ta ring. joda tace yayan hafsa
naga kamar dad ne yake kiranka, dasauri Ahmed
ya ajiye abunda yake yadaga wayar
Muryar amina yaji tana kuka bruhh kazo dad ne
bashida lfy sosae yama kasa motsi, what!?
Dasauri ya tsinke wayar yasaka takalmin sa zai
fita joda taci gabansa lfy yayan hafsa? Ahmed
yace dad ba lfy da alamu jikin nasa yayi tsanani,
joda tace subhanallah Allah yabasa lfy ameen "
gudu yake tamkar zai tashi sama , yana shiga
gidan yabude ganbun motar baiko rufe ba
yashiga dakin dad dinsu tin a kofa yake Jin
kukan hjy da amina
Gunsa yayi yadaga hannunsa yaga baya motsi
sann jikinsa yayi sanyi, innalillahi wa'inna ilai'hir
raji'un naji yafada, hjy tace ya mutu koh? Ahmed
yace noo dasaura amma sedai munje asibity,
dakanshi yacakumi dad dinsu xua mota sann
yakira Mahmud yagaya masa yace kar yafada wa
hafsa tinda tanada hawan jini, a asibity suka
hadu likitoci dayawa Akansa ciki harda Mahmud,
Ahmed kam kasa shiga yayi saboda yanda yalura
cewa ciyon yaxo da wani abu kamar dayan side
din jikinsa yamutu, haka kuwa ta kasan ce
Daga ranar Ahmed yazama wani iri gashi nan
dae, ga joda ga dad dinsu, dole Mahmud yadauko
hafsa yaxo sa ita asibity, bakaramun tashin
hankali tashiga ba yanda taga abbansu baya koda
motsi ne " kusan wata uku ana fama dole aka
dawo gida Ahmed yace lallae baza'a fita waje da
shiba se maganin sa yakare na wata hudu, dole
badan kowa ya soba ya hakura, abdallah ma tuni
yadawo gida , hjy da amina ne ke kula dashi
yanxu kuma sun daina sedai idan Ahmed ko
abdallah ko Mahmud da yanxu yazo shine zai
canza masa kayan su suke yimasa wanka sann
kuma su wanke masa kashi da fitsari , joda ma
itada hafsa agida suke wuni kullum saboda dad
su suke ragema si abdallah ayki,
Hjy tashigo dakin tasame bakowa a hankali
takalli dad, tayi yar dariya sann tace se yaushe
zaka mutu ne " rayuwarka batada wani amfani
aduniya oxygen dinda yake bakinsa tajawo zata
cire se taji anbude ganbu, dasauri tajuya Ahmed
yashigo aykuwa kyallen dake gefen kansa tajawo
tana dafa masa goshinsa , Ahmed yace sannu da
kokari hjy, hjy tace yauwa Ahmed Allah yabasa
lfy ameen " dakin ta taje takira amina tace ke
ayki zan saki akan mahaifinki, amina tace dad
kuma dayake a kwance wani ayki za'a Mar
Hjy tace inaso kisaka pillow ki ida mun shi,
ma'ana ki karasa gawar, dasauri amina tajuyo
what? mamma anya zaki shiga aljanna kuwa?
Wlh ko kiyashi bana iya kashe wa bare mutum
kuma dad dina hava mama, hjy tace shikenan
zancireki asahun yayana sann kisani babu ni
banu ke " amina tafashe da kuka hava mama
yazaki mun baki, ni nama fara zargin cewa kece
kika hadda sa masa ciyon
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�5鈨�
Hjy tace kwarai dagaske nice nan, amina tashiga
girgiza mata kai tana kuka, hjy tabude wadrop
tajanyo mata wata doguwar riga tabata tace
irinta joda tasaka kisaka irinta se dare idan kin
tabbatar da bata dakin sann kitabbatar wani
yagan shigar ki kokuma fito warki adakin , umarni
ne ba shawara ba, amina taci kuka kamar ranta
zai fita daga gurin tafara nadamar kasancewa
yar hjy
Dare yayi su hafsa sunyi sallar isha itada joda,
joda tawuce dakin Gwaggo hafsa ma tayi dakinta
dake gidan, amina dake labe tawuce harda hada
jiki sukayi da hafsa, hafsa tace ke joda lfy wann
saurin haka , amina dataki juyowa tadaga mata
kai, sann tashige dakin,
tadade tana kuka sann tace kayi hakuri dad wlh
ba laifi na bane hjy ce tasakani, tana kai nan
tadauko pillow ta aza masa aykuwa yafara
Shure2 har dae yadena motsi tana ganin haka
tafita aguje, ba'a Fi minti uku ba Sega joda
tashigo dakin, pillow din datagani Akansa yabata
mamaki hannun ta takai zata dauke Sega hafsa
tashigo , ido tazare sann tace joda mezan gani
haka
Joda tace hafsa haka nasamesa wlh, hafsa tayo
Gunsa dasauri ta dafa girjinsa taji baya motsi,
dasauri tajanyo joda tana dukanta joda tashiga
kwala ihu, macuciya azzalimi ki rasa dame zaki
saka mana se wann " Ahmed yashigo dakin
dasauri , dakyar yasamu ya kwace joda a hannun
hafsa, sann ya wanketa da mari, bakida hankali
ne zaki kasheta ne ma tayi miki, hafsa cikin
muryar kuka tace Ahmed! Ta kashe mana dad da
idona nasameta tana danne sa da pillow
Ahmed yace what yajuyo gun joda yana jijjigata
joda tell me gaskiya ne abunda tace , joda kam
kasa mgn tayi sema kukan datake yi, Ahmed
yakwanketa da mari sann yayi ball da ita yaje
gun dad dinsu yaduba shi, ajiyar zuciya yayi
ganin akwai sauran rayuwa agunsa amma ba
lallae bane ya tashi danko yayi nisa , Hjy da
amina suka shigo dakin hjy tace lfy nake jin
hayaniya, Ahmed yace bakomai, hafsa tace hjy
joda joda zata kashe mana dad , Ahmed yace
daga yau kar wanda yakara shigowa dakinsa
gwaggo itace zata cigaba da zama dashi har
satinsa uku su cika sa'annan muwuce Egypt
dashi
Hjy tace gawar za'a zauna da ita, ? Ahmed yace
bai mutuba daransa , hjy tace what? Ahmed
kansa seda yajuyo yana kallonta sann ta basar
tace Alhmdllh bakar aniyarki ta biki, ana haka
Sega Mahmud da abdallah sun shigo aykuwa
dasauri taje ta rungume abdallah tana son kagan
joda koh dayanxu ta kashe dad dinku , abdallah
yace me, Mahmud kamar ya? nan ta zayyane
musu komai,
abdallah yakalli joda yace joda yaushe kika
canza, Dan ya aura miki dansa bakyaso shine
zakiyi kokarin kaisa lafira kin ban kunya ,Mahmud
yabanka mata harara yace butulu munafuka, joda
taje dasauri tarike masa kafa hava ya Mahmud
kafi kowa sanin waye ni wlh ahaka nasamesa,
hafsa ta turata dakarfi tace karki sake taba mun
miji tinda ke bakisan muhimmancin auren dayake
kanki ba ........
Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours ago
Pharidah Ahmad
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�6鈨�
joda tace karku mun irin wann judge din wlh
tallahi bani bace, abdallah yace kedai kika sani,
ana haka Sega wani yadanna bell din parlor
hafsa taje ta karbo sako envelop ne kamar
hotuna ne aciki akace tabawa Ahmed, bata duba
ba tabawa Ahmed yace menene joda tace cewa
akayi nabaka, Ahmed yabude abunda yagani
yasaka shi shock dakyar yakai karshen hotunan
noooo yafada acikin lion voice dinshi yacakumo
wuyan joda idonsa jajir ya dinga buga kanta da
bango dakyar Mahmud da abdallah suka kwache
ta
Hotu nan suka dauko suna dubawa innalillahi
wa'inna ilai'hir raji'un naji sun fada Mahmud yace
I hate you joda I hate you, abdallah yace I hate
you too, hafsa ma data gan hotunan tace hate
you again fasiqa kawai, dakyar tadaga hannunta
tajanyo daya daga cikin hotunan, hotonta ne tana
sanye da towel hannunta ajikin wani kato bakyan
gani, Ahmed yace me wann gardin yafini da shi
miye amfanin......hawaye nagani suna kwarara a
idon Ahmed abunda bantaba ganiba
Hafsa tace wlh wlh bazaki kara kwana agidann
ba ke koma abakin gate dinn kika sake lekowa
sena saka anmiki Dan banzan Duka, hafsa tace
oya Ahmed kasaketa kuma uku, Ahmed ya girgiza
kanshi am sorry hafsa amma babu saki acikin
aurenmu, sedai kuma kisani yanuna joda
banyarda da wann cikin ba kije kinemo ubansa,
joda ko motsi batayi gata nan dae haka
hafsa tajata tafita da ita har gate tamata korarar
Kare amina abun duniya ya isheta, tasan wann
ma makircin uwarta da mansura ne " gwaggo
bakaramun tashin hankali tashiga ba tayi kuka
kamar me lokacin dataji lbrn hafsa tace gwaggo
kina nan amatsayin uwarmu kanwar
mahaifiyarmu baxamu kikiba Dan yarki tamana
laifi gwaggo kam da bataga hotunan ba Sam
baxata yarda ba,
Daga ranar rayuwar joda ta lalace, haka zatayi ta
zuwa gidan hafsa kullum tin safe har marece
amma baza'a barta shiga ba tayi sintirin zuwa
gurin Mahmud shima ko kallonta bayayi khalthum
ma ta guje ta, gwaggo tace bata son ganinta "
amina ce kawai yarinyar datake jin sanyi agurin
ta tana taimaka wa joda batareda sanin kowaba,
dad yafara samun sauki saboda yanda gwaggo
ke kula dashi har yafara bude bakinsa dakanshi ,
mansura tafito daga wanka Sega joda tafito
itama rike da cup ta tsiyayo vita milk
mansura ta kwace ta zubar, sann tace baki isa
kici abun dadi ina agidann ba ana haka Sega
Ahmed yaxo, tsawa yadaka wa joda, ke Dan
ubanki banga ya miki cewa idan nakara ganinki a
parlor dinn sena karya kiba, joda tajuya cike da
kwalla tashige dakinta tafada kan gado tana
kuka, kwana take sallah yini take sallah tana
kaiwa Allah kukanta akan wann ibtila'in daya
sameta......
Muje zuwa
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
9/29/16, 12:32 AM - Queen Safiyyert馃憫: FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�7鈨�
Kwanakin sunja , watanni sun tafi cikin joda
yagirma wata takwas wanda yayi girma kamar
yan hudu ne aciki dakyar take tashi, joda duk
tafita hayyacinta, gwaggo kuwa itake cigaba da
kula da dad wanda sukayi 2month Egypt baiji
sauki ba dole suka hakura suka dawo gida , hjy
kam tafita har kasa se sha'aninta take , amina
kuwa kullum adakin take wuni sekuka take
gwaggo zatayi ta lallashinta har tayi shiru
Khalthum nagani da abdallah sun fito super
market sunyo siyayya, kai daganinsu kaga
masoya, joda zaune a parlor tafito daure da zani
se vest saboda duka rigunanta sunyi mata kadan,
agwaluma take sha tana hawaye, Ahmed yayi
sallama amma Sam bata jiba, ido yabita dasu duk
damuwa datake ciki bata hanata yin kyau ba
cikin ya karbeta sosae, wani abu yaji lokacin
daya kae dubansa ga boobs dinta wanda suka
kara girma da tsayi , kamshin turarensa taji
hakan yabata tabbacin shine tana juyowa yayi
sauri yakauda kansa , dakyar da cizon lips ta
daga tana ta nishi daki ran wai wai
Gabansa taci sann tace zanje hospital anjima
2dyz danka baya motsi, mari yawanke ta dashi,
kana yace so nawa zangaya miki cewa kidena
dan ganta danki da jinina , to bara kiji tin wuri ki
sake tunani kije kinemo ubansa Dan wlh baxan
masa suna ba, joda tadaga kafada tace it's of to
you, zamana agidann saboda nareni abunda ke
cikina ne kasani bantaba son abunda ke cikinaba
kasancewar sa jininka, saboda bana sonka, ina
haife shi zan bar maka shi sann inyi tafi yata
baxaku sake ganina ba
Zakiyi nemana ko da a mafarki ne saboda kubani
sedai lokaci yakure muku, tana kai nan ta juya
tawuce har tabude dakinta sekuma tajuyo, tace
Ahmed! abunda bantaba jiba joda takira sunan
Ahmed, wlh wlh jininka ne danka ne ko yarka,
ban yiwa dad din hafsa komai, hannu tadaga
sama tace ya rabbi kada ka karbi rayuwa ta baka
nuna mun wanda yakulla mun wann sharrin ba,
ya Allah kada ka karbi rayuwa ta baka nuna mun
nadamar wadann bayi na kaba wadanda kasa ta
rufe ma ido suka manta waye joda suka manta
kyawawan halayenta suka manta dacewa bincike
shine gaba before a yanke hukunci
Jikin Ahmed yayi matukar sanyi, yarasa ma
wanne tunanin zaiyi, dakinsa yaje yakwanta kan
gado ya dubi sama, ya Allah ka dora ni akan
gaskiya nakasa yarda dakaina tin randa abun ya
faru nakasa yarda 100% sedai kuma bazan iya
manta wann muna nan hotunan nata ba........
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�8鈨�
A asibity suka hadu da amina atare suka shiga
tayi matukar mamaki ganin doctor dinta yabata
hakuri akan cewa yayi tafiya sann suka dawo
fada akan yaushe tayi aure har ta haihu, joda
tace wann yanada tsawo gaskiya yanxun dae ka
duba ni babyn baya motsi, doctor yace amma
yanaga cikin kato kodai twins ne?
Joda tace eh haka suka ce nima kuma cikin yana
mun nauyi kuma suna wahaladda ni da yawan
motsi, haka dae yaduba ta yabata magani sann
yace haihuwar ta nakusa fist month tazo asibity
haka suka dawo gida amina tawuce gidansu tuni
tacire wa rayuwar ta duk wata damuwa sedai
abunda ba'a rasaba sann tadena daukar rainin
mansura da Ahmed duk abunda suke mata
rawawa suke,
amina ce ke kwantar mata da hankali sann tace
insha Allah tamata al qawarin cewa zata fallasa
asirin wadanda suka mata sharrin dazaran ta
haihu , shi isa tarage wa kanta tunani abun
aranta , aranta kuwa tana mamakin yanda amina
ta sauya lokaci guda, kamar va itaba kullum
setayi wa joda kuka tana neman ta kafara, joda
tace ay ko jiya kin roka kuma nace nayafe miki
Bayan yan kwanaki, Ahmed yatara taron gidan da
duk wani family na gidan , ciki harda gwaggo,
Ahmed yayi gyaran murya yace dalilin tara ku
anan shine, ina son sanin inda ake shiga da kudin
dad, abdallah yace yauwa bro nima abun naci
mun tuwo a kwarya, hjy tabuga tsaki to mekuke
nufi sata akeyi kenan,
Ahmed yace yes dole afito da kudinsa danko ko
rabin dukiyar sa babu sann naga wasu takardu
yasaka hannu da sunan hjy taya zai mallaka miki
duk wann dukiyar bayan yanada yaya da yan
uwa, hjy tace kai Ahmed bansan zancen banza '
abdallah kanaji ana gayamun magana baxaka yi
wani abu ba
Abdallah yace mezanyi bayan gaskiya yake fada,
hjy tace wlh kar ka sake mun wann zancen
takardu dae yacika yabani kuma babu wanda ya
isa yatada zancen, Ahmed yadaka mata tsawa
karya ne wlh, I have free speech in diz house,
dole kiyi bayani, abdallah kam yakasa mgn dukda
yaji zafin tsawar da Ahmed yayi wa mahaifiyarsa
Murya sukaji daga sama nacewa photo copy ne
original na hannu na, kowa yazare ido hafsa
kam Dagudu tayi hanyar waje Ahmed yace dad
ar u? Dad yace yess kowa yaxauna nine nan dad
dinku, amma baxan zauna ba se ankira joda da
mansura, hafsa tace no dad bakasan abunda tayi
bane, dad yadaga mata hannu kar wanda yasake
magana akira mun joda kawai dz my order .
Ahmed yamike jiki a sanyaye yaje gidan, dakyar
yashiga dakin joda, dukda tayi mamakin ganinsa
amma seta basar tayi tamkar bata gansa ba
Ahmed yace kishirya muje gida dad na son
ganinki joda tamasa banxa seda yakara magana
sann tace wanda yamutu yana dawowa ne bayan
nakashesa, Ahmed yace kitashi nace kafun ranki
yabaci, joda tace wlh ba inda zanje, Ahmed
yafidda wayarshi yakira abdallah yace yabasa
dad, ya gayamasa tace bazata zoba , dad yace
abata wayar, Ahmed yace ungo gashi badan
tasoba ta karba , dad yace kiyi hakuri joda kimun
da'a kizo, joda tace shikenan dad zanzo Allah
yasa inji alkhairi ameen.........
9/29/16, 12:34 AM - Queen Safiyyert馃憫: FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�9鈨�
Mansura kam tace bazata jeba sekace wadda
tayi sata , Ahmed yace wlh zanci ubanki zaki fito
kosae na karyaki, dole sae dataga dagaske yake
tadauko mayafinta suka je, joda baya tashiga Dan
bata iya zama agaba , kwance tayi hancin ta
arufe bata san warin tiraren mansura, mansura
tace tokuma ubanwa kike rufewa hanci ?
Joda tabuga tsaki tsaki tace uban da yatanka ,
mansura tace ni kike zagi, ? Joda tace Y not ki
fara nikuma naqi ramawa tinda ba tsoron ki nake
ba, mansura tace dallah rufe mun baki, fasiqa
kawai, joda tace Alhmdllh ni dana tashi
fasiqancin da mijina nayi sann ba'a taba kamani
da kato ba, mijina a budurwa ta yasame ni, baku
taba sanin ni fasiqa bace seda nadauki ciki,
kuna bakin ciki dani saboda ke taki mahaifar ta
mutu saboda yagaji da daukar ciki ana zubarwa
Ahmed yataka burki dakarfi ya isheku yazaku
cikani da surutu , tsaki yabuga sann yaci gaba da
driving.
suna isa kowa ta bude kofa tafita har cikin parlor
suka shiga joda taki kallon kowa tayiwa kanta
guri daban nesa dakowa tazauna, amina taxo
tazauna a tareda da ita kowa yabita da kallo
barinma da akaga ta kawo mata vita milk tace
antynmu maman baby gashi joda tace tancuu, ta
karba tana sha , dad yayi gyaran murya sann
yace Ahmed! Abdallah! Amina! Hafsa! Mahmud!
Gwaggo!
Duka ina hankalinku yaje lokacin dakuka
wulakanta joda agidann shin kun manta cewa
joda itace silar shiruwar abdallah, shin kun manta
kunya da kawai ci irin na joda, ko kuwa dacan
joda tana bibiyar gardi ne " waya gaya muku
cewa tana iya kashe koda kiyashi bare mutum ay
hankalin ku alkalinku , Ahmed yace wait dad
bantari nun fashinka ba ya akai kasan wann? Dad
yayi murmushi yace duk abunda kuke akan idona
da hankalina ina jinku ina ganinku nadade dajin
sauki amma na boye lafiyata ne domin in gano
masoya na agidan sann in gano wadanda sukayi
wann aykin
ba joda bace taso kasheni ba, sedai bansan kowa
ce ce ba , alokacin, hjy kisani duk abunda kike
kirika tuna wa da Allah b4 bisa wann baxan tona
as irinki ba agaban yayanki amma na sakeki saki
biyu, naki yin uku ne saboda anyi hani da hakan ,
amina tafashe da kuka ha kika ranar wanka ba'a
boyon cibi , nan tazayyane musu duk yanda akayi
harda makircin da uwarta ke hadawa , hjy da
mansura zufa tashiga karye musu,
Wayar Ahmed tayi kara yaduba yaga ansaka
doctor habib yana dagawa yace sir zancen matar
ka gaskiya bazata iya daukar cikiba saboda
mahaifar ta mutu sann tana da ciyon sanyi da
ciyon daji wanda yake lalata al'aurar Dan Adam ,
wann yaron dasuka zo inaga kamar agaresa ne
takwasa saboda yanda saka makon yanuna, wani
gardi ne yashigo gidan aguje yana haki yafadi a
capet yana Dan Allah ina joda kimun rai
kiyafemun tin randa , hotunan sukazo gidann
nakasa barci
Se mafarki nake zaki kasheni keda abunda yake
cikin ki, abdallah yace kai shut up waya baka
izinin shigowa nan dakin, kuma miye hadin ka da
joda? Gardin yace nine wanda aka mana hoto da
ita lokacin tafito wanka sena sheka mata powder
tayi bacci shine nadora hannunta a jikina aka
mana hoto , abdallah yace waya turoka kayi
haka? Dasauri ya dubi mansura wadda jikinta ke
bari yace wann ce, Ahmed yayi tsalle yaka mosa
ya dinga dukansa kamar zai kashe sa, why ar u
runing my mrrg , seda yafarfasa masa baki da jiki
, babu wanda yayi kudurin rabasu yanda zuciyar
Ahmed yabaci hau kam kowa yana iya hallakawa,
hannuwan sa biyu da kafarsa babu wanda bai
fasa ba haka ya dinga zubar masa da hakora
sann yakoma kan mansura seda dad yamasa
rantsuwa
A hankali Joda tamike tsaye tace toh hafsa se a
kiyaye gaba bincike shine gaba kafun hukunci, a
dena manta halin baya, Mahmud da abdallah I
hate u too kamar yanda kuka ce, sann ta juya ga
gwaggo, tace shikenan saboda wani yaki dana
nima sena manta tarbiyar dana basa, Ahmed
Alhmdllh da Allah ya bay yana komai bana
murnar ku karbeni ko ku yarda dani fatana kawai
kusan danku ne aciki na hakama ban iya kisa ba,
tana kai nan ta juya zata fita hafsa tace hava
joda ki tsaya mu fahimci Juna mana, joda tace
alokacin dakuka watsar dani kun kasa tsayawa
ku fahimceni so babu wann damar aguna, hafsa
tace plss joda kiyi hakuri
Joda tajuyo da karfi zatayi magana seta kasa
sakamakon murdawar da marar ta tayi, ihu tasaki
tafadi akasa........
Muje zuwa
ASEEYAH BASHEER ALEEYU
Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours ago
Pharidah Ahmad
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�1鈨�0鈨�
Ahmed yafito da gudu ya tallabi joda wadda take
ta bleeding kamar ruwan fampo, Ahmed duk
yarude se kiran dana yake hafsa da amina suka
karbeta abdallah yafidda mota Mahmud yaja
sukayi asibity , kusan likita yakai biyar akanta
ciki harda Ahmed, firr yaki yarda Mahmud
yashiga aciki saboda tsabar kishi, kusan awa uku
amma takasa haihuwa , Ahmed kam duk yazama
wani iri dashi yazauce, doctor habib ya fito yace
doctor Ahmed yarinyar nan fah takasa haihuwa
saboda batada wani sukuni dole anmata ayki
dasauri Ahmed yace ok bani file din nasaka
hannu
Karfe 3 dae2 aka shiga da ita operation room,
anhada komai za'a mata aykin Ahmed na gun
kanta yarike hanunta yana topa mata addua,
aykuwa segata tayi wani yunkuri danta yafado da
sauri Ahmed yaje yatarbe Dan bai daga ba Sega
daya yafado tareda komai da komai, Ahmed yayi
hamdala ga Allah yamika yayan gurin nurses din
su gyara su, yakoma kan joda dinki aka mata aka
bata allurai da magani tasha tea sann aka hada
mata ruwan wanka , amma kash dayan yaron
yakoma dama baifi 20 minutes ba yamutu, doctor
habib yace bata samun kulawa lokacin datake da
ciki komai ci take gakuma damuwa tamata yawa
,
Su gwaggo da hafsa tareda abdallah da Mahmud
sun shigo dakin joda na gaisawa da hafsa tana
ganin su takauda kanta gefe hafsa da kwalla
yagama cika mata ido " tajanyo hannun joda
zatayi mgn, dasauri joda tafizge hnnunta sann
tace karki sake tabani, nasanki ne? Mahmud yace
hava joda kaddara ce fa tariga fata, joda tace
shhhhh badakai nake mgn ba gaba danku kufita
bana son ganinku, amina tace joda harda
gwaggon taki, cike da bacin rai tace ehh har ita
lokacin da aka wulakantani harda ita kufita
naceeeeee
Dole kowa yafito yabata guri, abdallah yace plss
joda ki saurarenmu, joda tace ok ni zan fita in
baku gurin, Ahmed dake gefe yayi tagumi yarasa
mezai ce mata ga babyn se kuka yake amma ko
kallansa taki tayi, a hankali takoma kwance
tamkar tayi bacci, Ahmed yace kowa yafito, ruwa
ne kadai ake bawa yaron , joda kuwa tana Jin
shiru ta mike zaune tacire drip din da aka saka
mata duk ta yamutse dakin bataga metake nema
ba, can idonta yasauka kan wani file da hanzari
taje tabude takuwa yi sa'a akwai biro aciki atake
tafara rubutu
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�1鈨�1鈨�
Gida suka koma aka bar abdallah da Mahmud
khalthum ma dole tayi gida saboda yanda joda
tanuna tamkar bata santa ba, Ahmed yadawo
tareda amina tana rike da yaron bayan an basa
madara, dakin ta yagani abude, yace wa abdallah
wani doctor ne aciki? Abdallah yace bansaniba
muna masallaci yanxu muka fito , Ahmed yace
ok bara na duba, dakin yashiga yaga wayam
bakowa kuma duk an hargitse dakin, yaduba
toilet bata nan, tuni hankalin sa yatashi
Idonsa yafada kan guntuwar takarda dasauri
yadauko yana karantawa, ga abunda yagani
""""""Alhmdllh da Allah yabbayana mun gaskiya
da raina, saboda haka zan tafi bazaku sake
ganina ba, zama da mugun miji irinka hasara ne "
yanda ka tsaneni haka nima na tsane ka bana
sonka ko kadan, ga yayanka nan Allah yaraya su
" kasani bana bukatar koda yansu yanda kake
kina haka nake kin yayanka " Sai watarana" haka
kalmar tadinga masa yawo akai, ihu yabuga
tareda jodaaaaa , plss karki tafi kibarni
I can't live without you, you are my soul, my life
is in complete without you joda I love you I love
you so so much beyond your imagine. abdallah
yashigo dakin aguje yatallabo , Ahmed yace why
bruhh mekake yiwa kuka haka? Ahmed yamika
masa takardar, abdallah yace shittt, Ahmed yace
plss abdallah help kane momin joda, abdallah
yace relax bruhh indae tana a duniyar nan ko ina
ne wlh kamar mun sameta ne " amma ay
baikamata soja kamarka ace kana yiwa mace
kuka ba tin bayan rasuwar umma bantaba ganin
hawayenka ba se akan joda
Ahmed yace baxaka gane bane joda means a lot
to me world can not express how I fell about her,
Iove her with all my heart, abdallah yace kayi
kuskure daka maida so kiyayy, ana haka Sega
Mahmud shima bakaramun rudu yashiga ba,
Ahmed kam yakasa tsayuwa , abdallah yace kar
agayawa gwaggo abun zai mata yawa yanxun ma
tana cikin damuwa
kawai asaka nemanta tin yanxu, kowannensu
yafigi mota yabar asibityn Ahmed kuwa yazama
kamar tababbe , Karfe 5 tayi yaga basu dawo ba,
shima yafigi mota yabar asibityn har baima san
inda yadosa ba baikuma tsaya tambayar kowa ba
, yakai wani babban titi ne anan wata mota
tabigesa atake tasa motar ta gangara jama'a
suka kaimasa dokin gaggawa
Wayarshi dake ring aka dauka abdallah ne yakira
shi, wani mutum yadauka yayi masa bayani,
abdallah yace ya salam ashe ma yana gurin
taron daya taresa kenan dakyar ya kutsa acikin
mutane ya samu wani yakama masa Ahmed suka
saka shi a mota akayi asibity dashi..........
Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours ago
Pharidah Ahmad
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�1鈨�2鈨�
Anyi sa'a bai samu wani rauni ba sedan ciyo
dayaji a hannun sa, yana farkawa yafara kiran
joda, dad ina joda na, Dan Allah kace tadawo dad
kane momin joda in ne mata gafara, dad yadafa
kansa I'm sorry son joda zata dawo wasa take
maka, Ahmed yace hakane gwaggo?
Gwaggo da hawaye yagama wanke mata fuska
tace ehh ka santa dason wasa , ita kam ba batar
yarta yada meta ba halin da Ahmed yashiga sann
ga yaron ta tabarsa, Ahmed yaki cin komai yace
dole se joda tadawo zasuci tare jifa jifa zakiji
yace joda tadade sena mata duka idan tadawo ,
abdallah da Mahmud suka shigo dakin duk sunyi
gumi sun wani iri dasu
Da gudu hafsa taje ta rungume Mahmud tana
kuka ya Mahmud ba'a ganta ba koh? Mahmud
yace kiyi hakuri za'a ganta insha Allah, Ahmed
yace ay wasa take yanxun zata dawo xua 10,
seda kowa ya zubar masa da kwalla yanda
Ahmed yake da taurin zuciya bako wane abu
yake daga masa hankali ba bare ma har yayi
kuka, babynsa yaduba yace you koh " kaine
kabawa matata wahala har tayi fushi tafita Allah
idan tayi fushi dayawa zan baka punishment
tsallen kwado zakayi,
Abdallah kam fita yayi Dan bazai iya kallon halin
da Dan uwansa yake ciki ba, hafsa kam anci
kuka kamar me, hakama khalthum abun duk
yamaidata gata nan dae, Karfe goma na bugawa
Ahmed yace yeeee 馃槄 my cweet joda yanxu
xata dawo aykuwa yayi tagumi yana kallon kofa
har 10:30
yana jin anbude ganbu yace oyoyo joda ta.
amma me dad yagani tuni yabata fuska yafashe
da kuka dad kace xata dawo kuma taki dawowa
kodae bazata dawo bane? Iye kuka yasaka musu
tamkar karamun yaro se lallashinsa ake amma
kamar baya jinsu joda kadae yake kira
Yau kusan kwana hudu ba inda ba'a saka neman
joda ba, a ranar data bata seda Mahmud yasaka
aka rufe kowace ta shar garin amma komai
sunan joda basu samu ba , joda kam tana fita ta
nemi adaidaita tashiga se wata unguwa wadda
batasan ko ina neba , tana zaune tana tunanin
inda zataje kamar a mafarki taga hansai na Jan
mota aykuwa aguje taje ta na kwala mata kira ,
hansai tajuyo bazata taba manta wann muryar
ba, dasauri suka rungume Juna suna mamaki
basu tsaya dogon zance ba, suka shiga mota se
gidan hansai, joda kam tace abata ruwan zafi tayi
wanka tacanza kaya, sann tace hansai bani lbr ?
Hansai tayi murmushi tace kamar yanda kuka bar
daji muma haka muka bar gurin bayan mun fito a
gari se wani bawan Allah yakadeni da mota
Yakaimu asibity ana kula dani kasancewar
nasamu kariya akafa seda muka kae kusan wata
daya, daga nan muka je gidansa Allah sarki
matarsa da yayan sa masu kirki basu kyama
cemu ba lokacin da sukaji waye mu, daga nan
muka cigaba da zama agidan muna tayasu ayki,
yarda rufaida tanada kirki hakama dansa najib
sannu sannu muka saba har yasakani islamiyya
nafara shawa'ar boko dansa ne yasakani
in takai cemiki dae yanxu dansa najib nake aure,
joda tace wow lbrn kamar nawa itama tabata
nata lbrn ,hansai tace kamm amma joda kinga ja
rabawa wai yanxun kinada danyen jego ne lallae
kuwa zan gasaki da ruwan zafi, joda tace
kaniyarki hansai, hansai tace kullll kar in kara Jin
wann sunan sedai kije deejerh kokuma Arab
kamar yanda najib yake kirana da kanwarsa rufee
mai kyau kema daga yau zainab kokuma zee
baby, babyn Ahmed, joda tace Allah sauwake
mun dawani can.........
Muje zuwa
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours ago
Pharidah Ahmad
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�1鈨�3鈨�
Deejerh hansai tasaka mai mata ayki wato baba
rabi kula da joda komai itake mata wankan jego
dasauran abunda yakamata mai haihuwa tayi,
amma aranta tace dole na nemo su gwaggo koba
komai saboda danmu data bari ba mama al halin
uwarsa nada rai, gwaggo kanta boyewa take
amma damuwa ce fal aranta,
Ahmed kuwa hauka hauka yaka mashi bayada
abun fada se joda anyi cigiya agidajen radio da
TV amma shiru, yau har anyi sunan yaro ansaka
masa abbakar sadeeq, tareda auren gwaggo da
dad wanda su abdallah da Ahmed suka roki
gwaggo akan ta amunce ta auri dad dinsu , dama
kuwa naga suna kallon Lol.....
Joda taci ko sosae tayi kiba boobs sun cika riga
tam, gasu se tsiya ya su ke mata kamar me, yau
tafito parlor suna breakfast harda najeeb mijin
deejerh, Sega breaking news anayi, ansaka hoton
joda akan 1 million akan duk Wanda yasamota,
Ahmed aka nuno yana kuka yayi baki yarame duk
suma tacika masa fuska acikin 10dyz kadai , cike
da nutsuwa yake zancen plss joda nasan na
cuceki kiyafemun ki dawo agareni rayuwa babu
ke tamkar kifi ne aruwa,
wlh nayi nadama zan bauta miki keda soyyr ki
matukar xaki dawo agareni joda kin tafi kin bar
danki gashi zai mutu baya shan madara, anan
aka nuno yaron sekuka yake, hansai deejerh tace
woww najeeb kagan wani beau boi, Ahmed kuka
yake sosa please joda nasan kina jina dik inda
kike ki dawo gareni plss sekuma yafashe da kuka
, tuni jikin ta yayi sanyi yanda taga yaron nakuka
atake taji kaunarsa fiyeda tunanin masu tunani
aranta
Hansai deejerh tayi sauri tadauki number din
batareda joda tagani ba , tana shiga daki takira
number din Mahmud ne tamasa kwatancen inda
take tace tanada information akan zancen batan
joda aykuwa dasauri Mahmud yace ya rubuta
address din dankuwa tin randa tabata ko wanda
yaganta basu samu ba se yau
Abdallah yakira sukaje har gidan, dama najib ne
yabada wann shawarar, har dakinsa suke sun
gaisa sann yakira hansai deejerh, Mahmud yace
kamm hansai mai shinkafa ce ta goge haka, najib
yace kuttt inkara jin hansai bare shinkafa,
gabadai suka sa dariya. nan dae tabasu lbrn
komai,
Abdallah yace wai yanxu joda tana agidann ne "
deejerh tace sosae yanxu yanda za'ayi kuje kuzo
da Ahmed da boi din karku da kowa, anan dakin
zan ce taje ta dauko mun wani abu kaga daga
nan se yayi mata mgn Cox bana tunanin zata
saurareku bare shi, Mahmud yace right brain
dinki naja fah
Haka kuwa akayi Ahmed nata kiran ina zaku kaini
amma suka masa banza seda aka kai gidan sann
suka ce joda na ciki ka nutsu ka san yanda zaka
shawo kanta nasan kai smart guy ne " Ahmed
yace ar u serious? Abdallah yace wlh bruhh ay
baza mu maka karya ba, Ahmed yace shine kuma
baku bari nayi wanka na shirya ba ahaka xan je
gurin matata a hargitse, Mahmud yace yarage
naka inzaka je kaje inkuma epixy zaka yi toh
yarage naka
9/29/16, 12:40 AM - Queen Safiyyert馃憫: FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�1鈨�4鈨�
Dasauri Ahmed yabude ganbun motar zai rufe ne
yadatse kafarsa, seda yasaka kara Ahhhh.
....abdallah yace kayi a hankali karka halaka fah ,
Mahmud ya girgiza kanshi yace wann yarinyar ta
iya judging Sam banza ta xata iya haka ba,
abdallah nima wlh mamaki nake yanda brain
dinta yabata wann abin amma fah gara da
tamasa haka koba komai yanxu xata karbi yan
cinta
Har dakin suka kaisa sann suka fito yana
rungume sa sadeeq dinshi, najib yazo suka gaisa
yace bara ya izo masa joda din. tana zaune tana
shan kunun masu jego Sega deejerh tashigo tace
joda danxo plss dakin najib ungo wann key din ki
rufe mun kofar, joda tace naki xua ni kanwarki ce
dazaki ay keni , deejerh tace shikenan karki Je
din . joda tabuga tsaki bani key din kawai mutum
naxamansa dole se an tada shi
Dakin taje kanta ko Dan kwali babu zata rufe
kofar taji wani irin sanyi yafara ratsa ta sekuma
taji takasa tafiya kam shin Ahmed takeji ta ko
ina a hankali ta tura ganbun ta leka bayansa
kawai taga ni se babyn su dayake rungume
akafadansa das das tashiga dakin tana son ganin
ko waye,
Ahmed yaji sanyi nashigarsa hakan yatabbar
masa da joda na gurin a hankali yajuyo fuskarsa
fauke da hawaye, yace joda plss karki kara tafiya
ki barni plss joda tace waya kawoka anan
mekazo yi anan kazo ne kasake wulakanta ni
mekake da fasiqa jahila kazama kucaka yar daji,
sekuma tafashe da kuka , Ahmed yace plss joda
ki bani lokacinki koda na 15 mnt ne in miki
bayani Dan soyy dake tsakanin ki da manzon
rahma s w a
Joda tace shikenan amma wlh Dan ka soko mun
fiyayyen halitta ne " Ahmed yace nagode plss ki
zauna , joda tazauna Ahmed yashimfide sadeeq
saboda yayi bacci, dukawa yayi yarike kafafun
ta. yace joda Dan girman Allah kiyafemun dukkan
abunda namiki, kewai da kin dauka kiyayyar ki
tasa hakan wlh so ne kurum , tin randa nadora
idona a kanki a daji kina busa sarewa bansake
gane kaina ba
tin a ranar nake jin inada felenz sosae akan ki
bankara tabbatar da hakan ba seda randa na
dauko ki aruwa daga ranar komai yacanza
nakasa gane so da kiyayya ne dalilin dayasa kika
ga ina miki wasu ababen amma plss on my
kneel. Joda tayi tsaki tace dt x invalid excuse
bazaka mun zakin baki ba saboda matar da kake
tinkaho da ita kaga no ko wacece, Ahmed yace I
sure you not agree with me, buh believe me wlh I
love you bantaba gayawa kowace mace haka ba
kece fist nd last
Joda tace I can't believe how much you love me,
Ahmed yace why joda? Tace coz I never like you
. Ahmed yace you layer, joda tace dakarfi tace
kaikuma maudari ne Ahmed yace shikenan idan
zuciyata karya take bakina seya kasance mai
karya? Idan bakina yakasance mai karya idona
bazasu miki karya ba joda luk into my eyes , joda
taki kallon sa
Ahmed yadago fuskarta suna kallon Juna dasauri
takauda idonta, Ahmed yace mekika gani aciki,
joda tace plss n plss katafi Dan Allah , Ahmed
yace it's alright am living amma kisani I love you
. sann ni I have nothing more to say , all my
words end amma kisani danki yanada hakki a
kanki bai miki laifin komai ba kika gujesa a
lokacin dayafi bukatar ki " Allah bazai barki
ba.........
Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours ago
Pharidah Ahmad
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�1鈨�6鈨�
Yana kai nan yajuya zai yafita tareda daukar
sadeeq, joda tace Ahmed! yatsaya cak batareda
ya juyoba gabansa ta tsaya batace komai ba se
kallonsa take a hankali taduka tarike masa kafa
inda taga jini na zuba, rigar dake jikinta ta yago
ta daure masa kafar sekuma tajuya tabar dakin,
Ahmed yagirgixa kai yafita, dasauri suka taresa
Mahmud ya karbi sadeeq yasaka shi a mota
abdallah yace yade? Zata fito ne "
Ahmed yagirgixa kansa yace no shez waz beside
her self with anger, abdallah yace muje nasan
abunda zanyi , ciki yashiga deejerh tamasa iso
har dakin da joda take kwance take se kuka
take, abdallah yace kisani gwaggo batada lfy
sann ciyonta yayi tsanani batada abun ambato
se joda
Joda ki kiyaye fushin mahaifiyarki da mijinki sann
kiguji Hakkin danki .yana kai nan yafita, amota
yasame su, Ahmed yace me kace mata ne?
Abdallah yace kajira ta xua gobe zata xo, Ahmed
yace to Allah yasa su kace ameen joda kam
kasa komai tayi sekuka take taki cin kowani
abunci ,
deejerh tasata agaba se nasiha take mata tace
joda tinda dae kinga yayi nadama yabaki hakuri
yaduka miki yaka mata komai yawuce sann idan
bakiyi hakuri ba wlh zakiga bakyau samun miji
kamar Ahmed yanada wuya, yarigada yagane
kuskuren sa yanxun atafin hannunki yake se
yanda kikayi dashi, kihakura da yanda rayuwa
tazo miki ki gode Allah
Dakyar tasamu joda ta amunce akan zata koma
gida gobe shima din seda najib yasaka baki, tin
safe deejerh tagama hada musu komai, bayan
tayi wankan jego tasha kunun masu jego tashirya
cikin wata atampa black and white se karamun
hijab dinta , tareda najib sukaje har gidan, dakin
Gwaggo tawuce amma setaga wayam bakowa
dasauri tafito tayi parlor
anan tasame gwaggo kan kujera amina na
ajikinta tana mata tsifa, dasauri amina taxo ta
rungume joda, gwaggo tace wa zan gani kamar
hansai? Deejerh tace nidin ce gwaggo ya bayan
rabuwa, gwaggo tace Alhmdllh bismillah ku shigo
anan take bata lbrn yanada akayi tasamu joda ,
gwaggo tamata godiya sosae sann tace joda
angama fushi damu, joda tadukadda kanta kasa
batace komai ba
Hafsa ce tayi sallama dasauri joda tadaure fuska
, hafsa tace baxamu gajiba da neman gafara,
Dan Allah Dan Dan darajar fiyayyen halitta
kiyafemana kiyafewa ya yanxu ki dubi zumuncin
mu, joda tabuga tsaki takalli gwaggo tace
gwaggo yanaga kinkoma hjy dake haka, amina
tace ay bakisan yanxun gwaggo itace matar dad
ba, joda tazare ido ke bari wasa, amina tace wlh
rana daya akayi da sunan sadeeq,
Joda tayi murmushi aranta kuwa tace Alhmdllh,
gwaggo tace joda ina neman wata alfarma daya
agurin ki, joda tace hava gwaggo ni har akwai
abunda zaki nema agurina ki kaddara har
kinsamu ne " gwaggo tace yauwa yata Dan Allah
Dan Allah kiyi hakuri kidauki komai a matsayin
kaddara ki yafewa kowa sann ki karbi danki ki
yarda da mijinki, murya sukaji daga sama ana
saukowa dad ne shima yace plss joda, joda kam
hawaye yashiga sintiri a fuskarta dakyar ta iya
furta shikenan dad zan koma........
Muje zuwa
ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄
Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours ago
Pharidah Ahmad
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�1鈨�7鈨�
Sadeeq hannun joda tagama basa nono yaron
sewani like mata yake, tacewa amina ke karbi
danku wlh ko nayi ball dashi, amina tace tavv wlh
kuwa dana cire miki kafa yarinya ana haka Sega
Ahmed yashigo dakin amina tafita tabasu guri,
joda kam yitayi tamkar bata gansa ba , agabansa
ta kwabe kayan jikinta which menz kenan bata
ma san dashi ba, Ahmed yayi matukar mamaki
wadda koda vest bata bari yaganta amma yanxun
gata tana kwabe kaya agabansa
Toilet tashiga tafi kusan 40 mnt sann tafito
wayyo Ahmed har yafara bacci sann tayi
sallah taci abinci duk yana a gurin, nightwear
tasaka ta kashe light din dakin tabi lafiyar gado
firgigit Ahmed yafarka daga bacci, mezai gani
wai har tayi shirin bacci, Ahmed yace joda joda
tamasa banza gurinki fah nazo amma zaki
shareni
Wayarshi tayi ring yadauka tareda fadan hello
bae yakk 2dyz wlh nayi missing dinki, kinko san
yanda nake sonki hava yazarce misali babu wata
ya mace aduniya danake so tamkar ki, joda
tazaburo dakarfi takwace wayar ta dora akunne
ke tamba daddiya kwartuwa mai bin maza, to wlh
I nagaya miki kinesantar dakanki daga alkaryar
soyy ta zuciyar mijina bakowa acikinta se ni tuni
na rufe ta da babban kwado, sann najefashi
acikin babban kogi bakida yanda zakiyi ki gansa
ma bare ki dauko har ki bude ki shiga acikin
haram tacciyar zuciyar sa
Tsaki tabuga tajefa wayar agina, se huci take,
Ahmed yace ashe bakiyi bacci ba, haka kike da
kishi tabb gara kirage danni mijin mace hudu ne "
joda tace wlh baka isaba wadda ma kake auren
yanxu sekayi waje road da ita zan zauna dakai ,
Ahmed yace a iya sanina wanda kake so shi
kake kishi kina sona ne ? Joda tace tirrrr da
insoka wlh Ahmed karya kike sona kike kamar
zaki mutu dubi sona danye akwayar idon ki
dasauri joda tadena kallon sa, wlh kayi karya ni
bana sonka, Ahmed yajuyo ta dakarfi bakin shi
kawai taji anata seda nunfashinta yakusa
daukewa sann yasaketa yaturata agado take
care. yajuya yabarta agurin
Kwanci tashi yau joda har ancika arba'in hjybinta
da maman khalthum sun sata agaba se bata
kayan mata suke tasha gyara kam kamar me,
Ahmed kam yaga wulakanci kala kala a gurinta
har yayi alkawarin bazai kara koma wa a gurinta
ba, musamman data gaya masa bata sonsa
doctor dinta take so " kwance take tana kallon
kunshin da aka mata yayi matukar kyau itada
khalthum kasancewar za'ayi bikin khalthum da
abdallah,
tuni suka fara shiri hafsa, joda amina khalthum,
Sallama akayi dasauri ta mike tsaye ganin doctor
a gabanta, joda tace mekazo yi anan randa
abubuwa sukayi mun tsanani ina kashiga? Doctor
yace karkice haka joda abbanmu ne bashida lfy
munje outside gurin treatment dinshi
Joda tace ok naji yanxun mekazo yine? Doctor
yayi gyaran murya yace nazo ne in kashe miki
aure sann na aure ki!!!!!!! Joda tazaro ido what
aurena kuma meyasa? Doctor yace saboda bkya
sonsa nikike so kuma baxan bari kicutu ba nagaji
daganinki a wahala, joda tace Allah sarki sedai
lokaci yakure mika wahala takare mun tinda
mijina nasona sann kuma nima ina sonsa fiyeda
zatoka.......
FULANIN DAJI N@ B Aleeyu 馃挄 page
1鈨�1鈨�8鈨�
what kina sonsa? Joda tace yes, yace amma
baki taba gaya masa ba koh? Joda tace ehh ina
tunanin gaya masa ne idan nazauna dashi naga
komai normal . yace nikuma nawa son yazakiyi
dashi? Joda tace zanyi kokarin ganin na kauda
shi in fuskanci na mijina, kafadunta yarike karya
ne joda sona yafi na Ahmed tasiri azuciyarki ,
joda tace ko kadan naka daban nasa daban ,
nahada jini dashi sann kuma jinina ne tagefen
zumunta, doctor yace na lie kokin manta jinin
jikina ke yawo a jikinki ne? Joda tace ban manta
ba Allah zai baka wadda yafini insha Allah wish
you all the best, yace alright shikenan zan wuce
amma kafun nan yau zan bude miki fuskata kigan
ni yanda ko a mafarki zaki iya she da ni
Juyawa yayi yacire face mark. joda kam duk
takagu yajuyo barinma dataji sanyi na ratsa ta,
yana juyowa joda tace you....ya....yan
haaffffsaaas dakyar tahada kalmar sekuma
tazube kan gado somammiya , toilet yashiga
yadebo ruwa ya watsa mata sann tafarka
takureshi da ido " abubuwan da dawo mata akai
hawaye ne suka fara mata zuba
Ahmed yace menene abun kuka kuma? Joda tace
nakasa yarda da abunda nagani ne " Meyasa
kaboye mun kanka kazo mun da fuska biyu?
Ahmed yace nima bansaniba joda tace then what
did you Ahmed yace birthday dinki skull dinki
kula dake hospital suturarki da duk wani abu
dakikaji ance oga to by nine. dasauri joda
tarungumesa tana kuka ilove you yayan hafsa,
Ahmed no karki kara cemun yayan hafsa yayanki
dae,
joda tace ok yayana, kanka meta yayi suka dade
ahaka sann tace nifa wlh se amun bikin aure
kamar yanda ake yiwa ko wace mace sann nima
akaini gidan mijina, Ahmed yace shikenan kikeso?
Joda tace eh sekuma zancen karatu, Ahmed
yace no bayanxu ba sekin gama bawa babynmu
abinci tukun haka dae suka wuni a ranar makale
da Juna sewani nan nan yake da ita joda kam
jinta take tamkar sarauniya yanda ake nuna mata
kauna zallar abin gwanin sha'awa
Kamu aka shirya naji da fada bakaramun kudi aka
zuba agurin ba , haka sukayi dinner itama abin
basauki aka dawo last walima dare aka kai
kowace agidanta amarya khalthum da abdallah
se amaryar 脳 joda 馃槄 hafsa kam ana gefe se
laulayi ake joda se ramawa take tana mata tsiya,
Joda tagama bawa sadeeq mama Ahmed yashigo
rikeda leda yakarbi Dan yakaishi dakinshi tareda
innah mai renonshi yatofa masa addua sann
yawuce, sallah sukayi suka gode Allah tamkar
fist night, sukaci suka sha sann suka bi lafiyar
gado acan aka raya sunna bakaramun so yanuna
ma joda ba itama haka
Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours ago
Pharidah Ahmad
FULANIN DAJI
N@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�1鈨�9鈨�
Dasafe bayan sunyi wanka suna breakfast
Ahmed yace wai ni in tambiki joda dama mace
idan ta haihu dadi take karawa ne " joda ta
kyalkyale da dariya tace nikam bansaniba, Ahmed
yace tabbb kinji ki kuwa tamkar honey, joda tace
kai kuma kazar ce honey din. Ahmed yace au har
kinsan dadin abun dasauri tarufe fuskarta tana
dariya no nikam wasa nake,
Ahmed yace bawani nan kinata cewa wayyo
mijina, joda tace kai yayana bansan sharri ni
bance komai ba, dae2 nan seda innah tafito da
sadeeq an shirya shi tsab Ahmed yakarbes
yamasa kiss gud mrng son, Ahmed yace kinsan
me , allah ya soni kadan inyi asarar mata yar
aljanna kamarki, joda tace tabb nice dae nakusa
nayi asarar handsome like you daya tamkar da
dubu,
Ahmed yajata sukaje dakinshi yaciro mata wani
dankwali yabata yace zaki iya tuna wann? Joda
tace wow amma ka iya ajiya harda stones din
jigidana ina xua nima dakinta taje tadauko jacket
dinshi tasaka tana xua tace bae nayi kyau
Ahmed yace how sweet tamiki kyau sosae anma
meyasa kika aje, joda tace I dunno kawai idan
anbata mun itake sanya ni nishadi babu wani
blanket dayake hana mun jin sanyi tamkar ita
Ahmed yayi murmushi yace Allah yabar mun ke
queen of my heart Haka abun ketafiya komai
normal tuni Ahmed yasaki mansura bayan
angano tanada cutar HIV AIDS dakuma cancer ta
mai haifa, allah kara kiyayemu,
Ahmed yashigo dauke da sadeeq wanda yazama
tubarikallah dashi wata uku amma kamar yayi 7
mnt bul bul dashi , joda nazauna tarasa yau kam
meke damunta , Ahmed yace hello maman
unborn baby, joda tace wlcm lion bae, Ahmed
yace wai meyasa kike cemun lion bae, joda tace
saboda komai naka tamkar nasa ne musamman
voice. Ahmed yayi murmushi yace toh mai ciki,
Joda tace wani cikin kuma Ahmed yace
amatsayina na doctor na hango babyna a jikinki,
joda ta bare baki impossible wlh wata uku
insaka samun wani cikin Ahmed yace ay se kiyi
amma akwai babe ajikin ki aykuwa tuni tafara
bubbuga kafa tana shagwaba,
Ahmed yace dama abunda nake so kenan kin yin
kyau da wann yanayin , ayko dakyar yasamu kan
joda da tace se ancire cikin seda taga Ahmed
yafara masifa da ita sann ta hakura wani sabon
tattali yadawo sabo, magani mai kyau yake bawa
sadeeq ba abunda yasamesa, sema kyau daya
kara , hafsa anjuye baby boi mai kyau dashi
Khalthum ma an dauka, anyi bikin amina da Dan
commissioner wato umar, inda sukaje dubai
honeymoon. Gwaggo nagani asibity wai anjuye
twins mace da namiji, joda tace gaskiya ya
Ahmed acirewa gwaggo mahaifar ta. Ahmed
yace why? Joda tace abin kunya ni na haihu ita
ta haihu, Ahmed yace bakida hankali kawai bata
gama haihuwar ba se acire lokuma ance miki mu
bama son kanne ne gashi ma koya wa bamuda,
joda tagwaguda baki tawuce tabarsa,
Bayan anyi sunan twin din gwaggo wato arif da
amra, gwaggo tanemi alfarmar yamaida hjy
agidan, dad yace sedai kinemi wata alfarmar
amma banda wann kusan sati uku tana biyarshi
dole yatara family meeting yanemi shawarar su,
Ahmed yace idan kana sonta ka maida ita dad,
abdallah yace dad hjy tayi nadama sosae Dan
Allah kamaida ita nidama kawai banda bakin
dazan nemi wann alfarmar ne "
kowa dae yabada go ahead. dad yace shikenan
bawani jimawa yaje yayi magana aka maidata
zama suke nakauna da amana itada gwaggo
koyaushe arif na gurinta gwaggo kuwa amra ,
wanda kamar sun raba yayan ne " dad na
matukar farin cikin hakan yanda suka hade kansu
sosae sann baka gane Dan wane sun dauki su
hafsa tamkar nasu
Bayan wata biyar cikin joda yagirma , sadeeq
kuwa har an iya tafiya joda tamatsa akan seta
cire shi a mama Ahmed yace samm seya cika
shekara daya dole ta hakura da hakan , wata tara
cib dasamun cikin joda tahaifo babynta mace
mai kyau tamkar balabara, Ahmed yarasa inda
zai sakata saboda dadi aka sakawa yarinyar
aisha suna ce mata aysha, honeymoon sukaje
daga can zasu wuce saudiyya, uhm...acan joda
takara kwaso wani cikin aysha na wata biyar
currr Ahmed yaki gaya mata kar tasamasa rigima
Har suka dawo bata saniba , seda taga cikinta na
girma sann tafara korafi aykuwa dataji akwai ciki
kamar zata buga ihu, Ahmed yace shikam idan
tajuye takara daukar wani yaya yanxu akafara,
****** BAYAN SHEKARA UKU*******
JODA rungume da aysha tana gyara mata kanta
Sega sadeeq yashigo rikeda kaninsa ameer yana
masa wasa Ahmed yakarbesa yana basa
chocolate, Ahmed yace madam waike bakya
tsufa ne haihuwa uku amma ko boobs dinki sunki
juyawa ma bare skin dinki ollwyz fresh kike
karawa, joda tace kaima ay nima wlh allah tsoro
nakeji kar wata tamun snach gaka tamkar
saurayi kullum, Ahmed au na manta ingaya miki
fah commissioner yabani yarsa safina, joda tace
what? tura aysha tayi ajikinta tawuce sama
aguje, Ahmed yace yau nadebowa kaina rigima,
dakyar tabude masa ganbun yajanyota sekuka
take halshensa yasaka yashanye hawayenta sann
tace relax April fool ne " joda takai masa naushi
kaiko Allah bana so kadena " Ahmed yajanyota
ajikinsa kece tafarko kece ta karshe agareni joda
tace Allah koh? Ahmed yace nima Allah kara
rungumesa tayi I loves you so much mu husband,
Ahmed yace loves you too my wife, Sega su
sadeeq sun shigo Ahmed yace kugyara zamu
dauki selfie
THE
END
TAMMAT BI HAMDULLAH , ALHAMDULILLAH,
Ina fatar adauki darasin dayake acikin wann
novel ba kyale2 cikinsa ba akwai sakon danake
son isarwa jama'a mai brain shiyake ganewa and
the last thing is Every Single Person On The
Planet Has A Story Don't Judge People Before
You Truly Know Them The Truth Might Surprise
You
All the best 馃憤馃徎
Godiya ta musamman ga duk wadanda suka bada
lokacinsu gurin karanta novel dina Allah yabar
zumunci da kauna, masoya a duk inda kuke ina
mika gaisuwa ta 馃憦馃徏
Godiya ga grps dinmu
excellent writers
sadau novels
M jabo novels
Dandalin karatu,
Hose of novels
Facebook fans
and others
Zanmika sakon ta'aziya ta ga daughter na kuma
frnd dita rookie sadau Allah yajikan kakanmu
daya rigamu gidan gaskiya ameen 馃憦馃徏
Kukasance tareda asiya Bashir Aliyu yar mutan
sakwkwatawa , marubuciyar
Haduwar WhatsApp
Azla
yar India
Abokina
Fulanin daji
Nd the nest x SADAUKI
Yaudara , cin amana, zurfin ciki , nadama, rashin
tausayi , maraici da kadaici, tsa gwaron soyy ,
sarauta duk sun tattara acikin sabon littafina
wato sadau ki, karka /ki bari abaki lbr
08122048543 for comments or corrections 馃枈
Bye luvz you so so much my fans.

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *