Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Sunday, July 8, 2018

JUYA Comple Hausa Novels (Dandalin Hausa Novels)

adsense here
JUYA Comple Hausa Novels (Dandalin Hausa Novels)
9/27/16, 7:56 PM - Messages you send to this chat and calls are now secured with end-to-end encryption. Tap for more info.
9/29/16, 2:11 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
1_A gaban mudubi take tana k'yali,ta shafa
nan,ta shafa chan,ta mudubin kuma tana d'an
k'allon ta cikin shi tana murmushi, ganin yadda
mutuminta ya zuba mata ido ta ciki.
Juyowa tayi,yai d'ai-d'ai akan gado yana
k'allonta, d'uk rashin k'yau na abu,toh mud'in
kana muradin shi mai k'yau ne a wajen ka.
Babban mamakin shi yadda ya kasa ganin munin
Matarshi a kullum, yakan shafe "seconds" dan
gano ta inda "Prettyn"shi ta gaza, kai ya girgiza,
dan shi baiga makusa ajikinta ba ko kad'an.
D'uk a kullum dangin shi suna mishi gorin d'uk
k'yawawan garin nan,amma ya rasa wacce zai
jaju6o sai Fulera,ga ta "JUYA",ta bare suce ko
dan haihuwa taci darajar so,,d'uk ta tare gaba,ta
tare baya, ta hanashi ganin d'uk wani makusa
tata a gare shi,balle yai tunanin gazawarta na
zama "JUYA".
Asalima shi in d'ai zai tozali da Fureran
shi"Pretty" toh yakan manta komai.
"Pillow" ya sake jawo wa,lokacin da ya g'yara
k'wanciya yana cigaba da k'allonta, d'ai- d'ai da
dak'ika d'aya baya fatan yaga "Pretty" ta
barshi,yana matukar k'aunar ganinta kusa dashi.
Bai aune ba ya ji ta hure mishi ido da bak'inta
tana murmushin nan wanda ke sashi murmushi
ko da bai shirya ba,, kamshin "lestrine" ya buge
shi, had'i da kamshin alawarta ta kullum,"splash".
Take ya sau ajiyar zuciya, kan ya k'allota.
Hakika yana kara godiya ga Allah mad'aukakin
sarki da ya bashi "Pretty" a matsayin "Matarshi"
kuma "Sanyi ga Idanunshi". Tabbas yana daga
cikin maza masu t'sant'sar sa'a a rayuwa na
samun "mace ta gari'',wacce ganinta kad'ai, ya
isa wanke maka bak'in cikin rayuwa,har yai
hamdala da mahaliccin shi,dan ya mishi
baiwa,irin wacce ba Kowanne namiji ke da ita ba,
a ganin shi,dan ya hanashi "D'a" bazai zamu ya
masa butulci ba.
Murmushi ya sakar mata,kamar kullum ya fara
yaba mata wankanta. "Kinyi k'yau sosai pretty, a
kullum ranakun duniya kamar ana dad'a kawata
min ke ne,kamar ki zauna nai ta k'allon ki kawai.
"Ko zaki fasa zuwa sunan?
Murmushin jin dad'i tai,gashi d'ai kullum irin
kirarin nan tana shan su,amma baya hana taji
dad'in jinsu.
Zama tai, tare da ruko hannunshi ta kai baki
tai"kissing" take k'wa ya sauke ajiyar zuciya,tare
da d'aura d'ayan hannunshi kan nata..
Tsaf ta riga da ta gama samo abinta cikin ruwan
sanyi, ta riga da ta gama sanin d'uk wani "week
points" nashi akanta, mai lafazi mai k'yau ce ita
da sanyin murya, takan ko'k'arin tauna
zance,sannan ta ya6a mishi"gold" da "lu'u-lu'u
kan ta bashi.
Cikin salon ta da wata irin murya ta fara magana
tana lumlumshe mishi ido da d'an lallashi. Ji yake
mar rad'a take mishi a kullum.
"Kar kaji kom "Nawan" ni taka ce ai,k'walliyar ma
taka ce, zan rintse ta ga ganin kowa,sai d'ai in
mata y'an uwa na, badan sanin mahimmancin
sunan nan a gare ni ba,da zan ta zama,kai ta
k'allo na,har sai kace na ishe ka.. Ta karasa tana
fari da idonta, take k'wa ya sau ajiyar zuciya.
Unguwa ko bai niyar barin prettyn shi ba,da
kalam kawai zata sa ya firta "Toh".
Kai ya girgiza kan ya tashi ya zira rigarshi.
Ita kuma ta sa hijab da Nikaf dan rufe k'walliyar.
Tafe suke a mota,suna ta faman firar duniya
cikin nishadi,har ya faka a kofar gidan
sunan,wanda matar K'aninshi take gare shi.
Hannunshi na cikin nata,tambayarta yake sai
yaushe zai zo d'aukan ta? Ganan wasu na
shiga,wasu kuma na fita a gidan sunan,sai d'ai in
sun fito,maimakon su tafi,sai suja su tsaya
k'allon su prettyn.
Tana shiga ta tsaya ta cire nikaf d'in, kan tai
bangaren mai jego.
Da sallama ta shiga d'akin fuska sake, fal cike da
jama'a, kowa ya zuba mata ido, ta samu gefen
gad'on ta d'an dosa na,tana kula da hararar da
wasu ke sakar mata,"ina yinin ku.. Fuska mai
jegon ta yamitsa,kan tace"sai yanzu? Dad'i Miji..
Murmushi tai,dan tasan da ta tofa yanzu za'a
fad'a mata magana. Cigaba tai, "shidai cin tuwon
kishiya ramako ne,ehee. Kai ta k'ada, lalle
mutum.
K'anwar mijin tace ta amshe,"ba Kowanne tuwan
bane na ramako..kar ma kisa a ka,a yadda tai
shirim d'in nan ne zaki sa rai? Baki ta ta6e,kan
tace suna ga wata wai "JUYA" tashi tai "parlour''
tana hararar prettyn,wacce ke mata murmushi.
By
Feenat Ja'afar.
9/29/16, 2:12 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 3_Asalin su y'an
Kaduna ne,a karamar hukumar Zaria,Baban ta
Muhammad "mechanical engineer ne,Matar shi
d'aya,Mama Dije,da yaran su takwas, tun samun
aikin shi ya dawo cikin garin Kaduna da zama da
iyalen shi,a lokacin yaran biyu ne rak!, Suleiman
shine babban d'anshi,sun dan jima kan su samu
Aisha,sai Furera,Maryam, Hassan da Husaini da
k'annen su. Tun su Furera suna yara Abban su
ya shiga "missed call" sai ya zamo baiya aikin
Gomnati sai makanikanci, rumfa ya bud'e dan
wannan harkar, ko dan burin shi na sai yaran shi
sunyi karatu, da taimakon Allah,da taimakon dan
uwanshi dake Zaria ya kafu,, sosai ya iya g'yara,
dashi yake samu ya biya ma yaranshi karatu.
Tun tashin yaran yai musu sa6on dad'i, sai kuma
akazo ya rasa aiki,d'uk da haka yana iya kok'arin
shi yaga ya wadata yaran shi da d'uk wani abin
jin dad'i, ta yarda bama zasuyi kukan baida shi
ba,d'uk an neme shi daga baya yace ya d'aina
bautawa Government, g'wada yaci da gumin shi.
Mama Dijee itama takan yi su su6o da sauran
kayan sanyi. Sosai suna k'wata ma yaran su
tarbiya,kuma sun taso ba laifi, d'uk dunsu ba
masu son k'warafniya bane,in banda d'aya da ta
fita zakka cikin su,wato "Fure". Tun tashin Fure
sam bata d'aukar wargi,ita sha yanzu ce,magani
yanzu,sam bata barin ta k'wana. Gidan haya na
biyu kenan suna yi,yanzu su biyu ne aciki,sai d'ai
shi baban su sai ya kewaye bangaren su da
langa-langa, d'uk ba jin dad'in zaman suke,d'an
fa d'ayar matar sam batta kirki, d'uk hakurin
Mama Dijee sai da ta kaita bango,a kan yaranta
t'saf sai taci damara. Ga yara zagi a bak'insu
kamar ruwa. " Fure ki wuce mu tafi yanzun nan
kan na had'a ki da Umma. Kara chakumar wuyan
y'ar gidan matar tai, "wallahi bazan cikata
ba,mey yasa zata zagi uwata? Sa'ar ta ce? Jin
kok'awar fad'an ne ya fito da Larai daga daka,
tuni Aisha tai gefe,dan tasan ba abinda zai hana
ta rufar musu a ka. Zaune ta samu Furera akan
y'ar tana nad'a kamar Allah ya aiko ta, sarai
Umma naji, amma tai kamar bataji ba, Larai batai
wata-wata ba ta rufar wa Fure,tana dukanta ita
kuma tana narkar y'arta, wanda a zahiri ta fita
girma da komai,amma ihu take a taimake ta a
hannun Fure. Ganin zatai wa y'arta illah yasa ta
bar dukan Furen ta hau ko'k'arin fincike ta akan
y'ar. " uwata Sa'ar ta ne,ai dama na fad'a mata
wataran sai na fasa mata baki agidan nan, shegu
dangin maguzawa... Da gudu ta zuba, ganin larai
taiwo kanta tai zaure, g'walo tai ma yarinyar, da
tana kuka tana kuwa k'wararowa iyayen Fure
wasu mugan zagi ba ko dad'in ji, tana daga
zauren tace "oho d'ai, ko banza na koya miki
hankali, kuma zamu had'u anjima. Umma dake
d'aki suna jin ruwan ashar din da Larai da y'arta
suke watso musu.. tai shiru ita da Aisha da
sauran k'annen ta. D'a ne ka haife shi baka haifi
halinshi ba,ko ta hana Fure kula Larai da yaranta
sam bata jurewa,barin in suka zage ta,amma abin
na yau yafi k'arfin ta,dan d'uk tsiya sai d'ai suyi
chachar baki,amma yau Fure harda dam6e. Tana
zaure har taga shigar Larai da y'arta d'aki kan ta
arto da gudu tai kewansu. Harara Umman ta
sakar mata, uffan bata ce ba tai shiru, amma
dole yau asan nayi, dan sam zaman gidan nan ba
nasu bane, dan tsaf Larai zata gur6ata musu
tarbiyar yara, musamman Fure, zama da Larai
bak'inta yai masifar kara bud'e wa,ga fad'ar
magana kamar y'ar makafi. Da dare kuwa Abban
su yana dawo wa ta kora mishi bayani, kamar
kullum ci kanki bai cewa Fure ba,wanda ita
Umman ta zata zai ja mata k'unne. Tun daga
ranar jaraba ba kama hannun yaro tsakanin
ya'yan Larai da Fure, sam bata ko shakkar
girman su, haka zasu kamata su mata taran
dangi har uwar amma uffan Umma bazata ce ba,
kuma inda zasu k'wana dukanta sai ta rama
kuma ba ko hawaye, tana zuwa d'aki Umma ta
kara mata wani. Ba shiri Abba yasai fili ya kuma
ta dasu a gidan Larai kan suka samu lafiya.
Gidan su kad'ai ne a ciki,mai d'aki biyu da
baranda, yanzu burin Abban su kawai ya tara
kud'in gini, dan k'warai ya gaji da bin haya,in
yaso ko na kasa ya gina musu. K'wance tashi su
Fure har an shiga secondary, day d'uk yaran
suke,yayinda Yayan su Suleiman ya kammala
secondary sai jami'a. Sosai y'an gidan suna da
K'wak'walwa, barin Fure uwar rawar kai, Kasuwa
kam ta bunkasa wa Abban su, dan har ya bud'e
wa Ya Suleiman shima wajen g'yaran kan ya
samu g'urbi a A.B.U Zaria. Anyi hutu suka
tarkata sukai Zaria ziyara, anan ta samo yaran
kawunsu sa'aninta suma sun dawo a Queen
Amina, yadda suke bata labarin makarantar da
"boarding school" kawai tai sha'awar zuwa,,
Uncle d'in nasu achan yake aiki d'ayan, tuni Fure
ta tada bal'li ita sai Boarding. Da taimakon
Kawun ta biyu da Abban su ta samu g'urbi a
makarantar Queen Amina College. Haka Abba
yake fafutukar nema kodan biyan makarantun
yaran. Fure a Boarding, k'warai rayuwar ta
mata,d'uk da tana k'ewar gida wataran, nan ido
ya kara bud'ewa, daga "Furera" ta koma "Pretty".
A d'uk dabi'ar ta bata nuna cewa ita y'ar wani
ce,asalima ita irin k'aryar nan ta y'an boarding
sam bata d'ad'a ta da kasa, dan sosai tana alfari
da Abbanta, kuma bata 6oye mazaunin ta d'uk
fafar ta. K'wance tashi ba wuya a gun Allah,ga
nan su Fure har an shiga SS1, Cikakkiya ce
Pretty,ta bun kasa,d'an ba ramammiya bace ita
sam, t'sirinta da tsabar iyayinta su ke boye
muninta, bata sahun farare, sai d'ai sahun
bak'ak'e, sai d'ai a cikin bak'ak'en ma iya kiranta
wankan tarwada, a fuska kam ba wata
k'yak'yawa ta azo mu gani bace, d'an karamin
k'yau gare ta, sai d'ai a jiki a dire take. Babban
sirrin k'yaunta" gashi" dan ko a fuska "eye
lashes" d'inta da girar ta sunfi d'aukar ta tazamo
mai k'yau. Yadda k'wa take far-fara su in tana
zance, kai kace da ga'iya take,dan tamkar tai
"fixing". By Feenat Ja'afar.
Like 路 2 路 Reply 路 Report 路 Apr 10
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 4_A jiki "Full option" ce
kam,abun da a yanzun tafi jin haushi a kira ta
dashi kuwa shine "Fure". Yana d'aya daga dalilin
da yasa a school suka k'ak'aba mata" Pretty "
dan kam ita k'yau ce da wanka. D'uk yanzu y'an
unguwa yawanci da Pretty suke kiranta, a gida
ne kawai sunan ya gagara k'arbuwa gun su
Umma,dama shi Abba bai san da sunan ba.
Ak'wai lokacin da Abban ta da ya Suleiman suka
je musu Visiting, shaf sai suka manto visiting
card d'in a gida. Da alfarma aka kira wata mate
d'in su Fureran kan su fad'a mata sunan ta kira
ta da y'anuwanta. Sunan ta tsaya tana maimaita
wa, halamar tama rasa mey shi, sai da yasa
sunan uba da unguwa kan tace"au Pretty ce, bari
na kira ta,, da d'an gudunta ta tafi tun daga
wajen ta fara k'wala mata kira, Abba ya girgiza
kai, kan ya k'alli yayan nasu,"yanzu wai kaji Fure
har sunan k'arya ya shafe na gaskiya? Murmushi
yai,kan yace"Abba makarantar kenan,sai a
hankali. Tana hango su Abban da gudunta ta
nufo su, har ta baro sauran a baya,"da gaske
k'wa kaga ita d'in ce suleimanu, dariya yai,
lokacin da ta karaso tak'wa tukuikuye Abban,kan
ta koma kan Yayan nasu. Bayan sun gaisa yace,
"Yanzu Fure ke ce kika koma pretty saboda
Allah? Da sauri ta matso tana marairaita mawa
baban kan ya d'aina cewa Fure,sai wai school ta
d'auka. Yace" ungo naki, shi dai ya Suleiman
dariya kawai yake musu. "yasu Umma? Yaya ya
makaranta? Yai murmushi, "suna gaida ku, " yaya
ka kusa gamawa ai? Kai ya k'ada mata,''InshaAll
lah, murna take kan yayan ta shima zai zama
engineer. Sunje hutu sun dawo,wanda a shine
suka shiga ss2,anyi sabin coppers, yayin da
iskancin su pretty ya motsa. Sun bala'in raina wa
coppers hankali, d'an su kam mayun mata ne.
Ranar d'aya ya shigo ajin,Hausa yake d'auka, sai
fafa yake musu shi nan a dole yana gaban y'an
mata. Bayan ya gama darasi ya k'allo su, dariya
kawai suke mishi, amma shi ko a jikin shi, sai ma
wage musu baki da yake. "If you hv questions
queshh" or additional information... Haba wa,mai
su Pretty zasuyi inba dariya ba. Har aka buga
"next period" ya bar ajin ba wanda ya kula shi
sai shakiyancin su suke. Yana fita su pretty ita
da y'ar desk d'inta suka fito k'waik'wayar shi,, ta
d'au alli"if u hv questions quashhhhh... Or
additional information. Yadda kasan shine a
gaban allon. Fad'i suke in banda malam,mey ya
kai turanci kai da kake koyar da hausa? Tuni sai
suka fara tariyo na d'ayan coppern da yai musu
mathematics, dariya Fure take harda rike
ciki,d'an yin irin in'inar da d'an NYSCn yake.
Tsitt! Ka ke jin ajin sai dariyar Fure da Adama ke
tashi. Zungurar ta Adama ta fara,lokacin da tai
ar'ba da abinda yasa class y'in shiru. Hard'e
yake da hannu a kirji,rike da "text book" an
rubuta"chemistry" a jiki,sanye yake da fara sol
d'in rigar NYSC da siririn farin glass a
fuska,fuskar nan sam ba annuri,, tunda suke ko a
malamai basa jin da wanda ya ta6a musu
k'warjinin wannan, balle a wanda suka raina. Ajin
ya shigo,har lokacin idon shi nakan Fure da ta
kame a gun baki sake, tuni ita Adama tasan
nayi. A gabanta ya tsaya tamkar wani soja rai a
had'e. Takarda Adama ta nannad'e,sai ta seta
Furen ta hulla mata, a tsorace tabar K'allonshi
tai gun zamanta. A t'sanake ya karewa ajin
k'allo, tabbas nan Garba ya shigo dazun,dan daga
iskancin su yasan sune, yana jin lokacin da
malamin Hausa yake sanar da sauran iskancin
da suka masa. Ya kai a k'alla minti biyar yana
karantar ajin su Furen,yana k'allo takadiran cikin
d'aya na zungurar d'aya. Kai ya k'ada, kan ya ju
ya kan allo ya fara rubutu. "Chemistry" Shine
abinda ya rubuta. Fure ta ta6e baki. Juyowa
yai,kan ya bud'e baki cikin murya mai sanyi.
Cikin turanci yace sunan shi "Ahmad Abba
Ahmad", shi zai na d'aukan su Chemistry daga
yau. Bayani yake musu,wanda tsit ka ke ji kamar
anyi ruwa an d'auke, dan d'uk iskancin su nasan
kure Malami a turanci yau sun gamu da bokan
turai. Class mastern su har zuwa yai leken ajin
dan jin yau shirun su da yai yawa, a tunanin shi
discipline master ne a ajin,da mamakin shi sai ya
ga Ahmad. Kai ya k'ada, lalle wai gaba da gaban
ta,Aljani ya taka wuta. Ko da aka tashi gulmar
Uncle Ahmad suke ta yi,daga suce mai girman
kai,sai su ce ya had'u amma. Suna hanyar tafiya
"hostel" suna ta shakiyancin su, kasancewar ss3
suna "practical'' a "hall'' yau su suke cin karan su
ba babbaka. Ko "lunch" basu tsaya k'ar6a ba
suka taho. A bak'in "gate" suka tsaya, ganin
Baba mai gadi na d'akin shi bai kuma gate d'in a
datse da "key", maimakon suce ya bud'e musu
su shiga,kawai sai suka hau mishi wakar su ta
kullum,wanda har ya riga ya gane su Fure. "
Baba a bud'e "gate" ko mu taru mu 6alla "gate"...
Shima kamar mai wakar daga d'akin nashi ya
basu amsa, "Ku taru ku 6alla,tunda gate d'in na
uban ku ne... Dariya su Fure suka sa, lalle ashe
mutumin su ne " on duty". Kawai sai suka bashi
amsa dan kawai suyi ta deban shi,, "K'warai na
uban mu ne,tunda Gomnati ta siya.. Da gora ya
fito daga d'akin yana bam-bami," yau zan kawo
karshen iskancin nan naku,, "au Fure? Nasan
kece gandi lida, yau za kuyi bayani.. Dariya suka
sa mishi," Baba namu,mukwa na Allah, muga
Annabi... Da gudu suka zuba, ganin ya bud'e gate
d'in yai Kansu da gora,, wuuu sukai "gate" d'in
kamar zasu 6alla suna mishi dariya,tun daga nan
aka fara yin d'ai-d'ai da kaya, daga su sai
underwear suka isa hostel. Washegari kuwa da
safe sai ga kira daga principal tana kiran Fure da
y'an Eysla d'ukansu.. Principal kam tasu ce,ba ko
shakka suka nufi office, sun san bazai wuce
fad'a akan surutun aji ba. Masinja ne yai kiran
Furen ita kad'ai zuwa ciki, yana zaune su biyu a
kujerar da ke gaban principal d'in, da ladabi ta
gaida principal, kan a ciki ta gaida su,d'ayan ne
kawai ya amsa,yayin da d'ayan ya d'auke kai.
Dagowa principal d'in tai,ganin Fure ce yasa ta
k'ada kai,"Furera" kai sunkuye ya ta k'warai
tace"Yes Mom, kai ta k'ada, kan tai murmushi, "
Trouble marker" kenan,ai tunda naji SS2 ne nasan
sunan ki sai ya fito ciki. "Wai zaku 6allawa Baba
gate koh? Kai ta kara kasa dashi, "sorry Ma, kai
ta k'ada, " ai kinfi kowa rashin ji, sannan kinfi
kowa tsoro. By Feenat Ja'afar.
9/29/16, 2:13 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 5_Tuni tai narai-narai
da ido kamar zatai kuka tana k'allon PCn, "Momy
kiyi hakuri, kai momyn ta k'ada, " last warning "
kar na sake jin haka daga gare ki "Fure" kai ta
k'ada, kan tai godiya tai waje tana murnar ba ko
"punishment". PC ta k'allo su Ahmad, wanda
suke k'allon yadda momyn ta bi Fure da k'allo
tana murmushi, " yaran sun matukar shiga raina,
tun jss1 d'insu aka kawo ni, tun a sannan nasan
dasu,fitina, tsokana,ilimi d'uk yan su ne. Kai su
Ahmad suka k'ada, tare da mamakin saukin kan
principal d'in. An dawo a break yake da su, d'ane
wasu suke akan desk a zaune, wasu sun had'a
group ana shewa, chan ya hango Fure a tsakiya
tana ta zuba k'wainane, kofa ya buga,da sauri
kowa ya nemi waje ya zauna. Kamar jiya,yau ma
ya kare musu k'allo, magana principal ya fara tan
tama na anya yaran suna da kok'ari? Akan Fure
ya dire idon shi wace ke fito da irin "Text book"
d'in shi a jaka. Ciki ya shiga,kan zasu gaida shi
ya zaunar su. Daga inda ya tsaya jiya ya
tashi,suna tsaka da karatu ya k'allo desk d'in su
Fure, ture-ture suke kamar wasu yara kanana.
Alli ya saita su dashi ya hulla musu, da hannu
yace su mike, kan ya tambayi sunan su, "Fure"
ya kira ta, da sauri ta daga tana k'allon Y'an aji
da har sun fara kunshe dariyar su, tuni ta kicin-
kicin da fuska kamar zatai kuka. Gaban allo yace
ta fito. Hannu ya hard'e tare da zuba mata ido
cikin glass,ita tuni hankalinta yai kan y'an ajin,
bata zata ba ta tsinci tambayar shi gare ta. "can
you name the first 20 elements of the periodic
table pls?" Tsayuwa ta g'yara,dan yasan dak'yar
in ma ta sansu bare ta rike su.. Sai d'ai kan ya
karasa zancen zuci ya tsinci muryar ta cikin
sauri-sauri tana jero su kamar ma ita wasan yara
ta d'au ka. "Hydrogen,Helium,Lithium, Beryllium...
Ba ko shan numfashi ta dire masa su tana du6en
shi. Kai ya g'yada, kan ya sake jeho mata wata
tambayar,kiris yake jira ya sata kneeling. "
electronic configuration of firs.... Da sauri ta
katse shi tare da karanto mishi, "Boron,carbon,
Nitrogen... Suma ta dire cikin sauri ba tare da ta
bari ya gama maganar ba,dariya y'an ajin suka
fara,tun itama tana dake wa har suka sa ta yi,
ajin ya k'alla, sai sukai tsit,itama ta kunshe tata,
bak'in kofa ya nuna mata da hannu, da mamaki
take k'allon kofar,wai tai "kneel down" ta daga
hannu ta rufe ido, tuni kuma ido sai ya raina
fata, dan taki jinin punishments,ga ya had'e rai
ba damar bada hakuri. Daga yin minti 5 ta fara
raki, shikam dalibai ya cigaba da koyarwa,jefi-jefi
yana d'an k'allo ta. Hawaye ta fara,da gefen
hannu take gogewa,gaba d'aya hannunta ya fara
sage wa, sai motsa K'afa take halamun ta gaji,
ya juyo da zummar kara k'allonta yaga tana
kuka, sai ya d'auke kai, y'an aji tuni aka shiga
taitayi,ganin Fure na kuka,dan sosai sunsan abin
da zai sa Pretty kuka babba ne. Ba'a fi minti uku
ba ya kara k'allo ta, ta cikin glass d'in ya d'an
rufe ido,bai so ta kaishi bango ba,kawai ya ki
jinin rawar kan nan na Fure ne. A hankali ya kira
sunanta ta bud'e ido, tuni har sunyi ja, d'aurewa
yai yace ta tashi taje ta zauna. A shag'wa6e ta
tashi tana d'an dingisawa, koh zama bata gama
ba aka k'ada, ya tattare kayan shi tare da d'an
k'allon yadda ta d'aura kanta akan desk hawaye
na zubowa. Da sauri ya d'auke kai dan kar su
gane yai waje, ai kamar jira suke sukai kan
Pretty suna lallashi. Har akazo k'wanciya in ta
tuno sai tai k'wafa, ita sam bata ga mey tai ba
da har ya sa ta kneeling. Shima d'ai Uncle
Ahmad d'in yana a d'akinsu dake cikin "staff
quarters" d'in, a ganin shi raini ne zaisa Fure yin
hakan,sai d'ai shi mai tausayi ne, tuno da yadda
take hawaye dazun d'uk sai ya ji ba dad'i. Ihun
y'an makaranta ne da ke "hostel" yasa shi tashi
da sauran y'an d'akin, tun zuwan shi wannan ne
na farko da akai ihun gardi,waje suka fitu,ganin
wasu malamai nayin hanyar hostel d'in yasa suka
bisu,ba kad'an ba yara ke gudu,wasu na fad'uwa,
d'uk anjijji ciwo wasu na kuka,kawai Fure ce ta
fad'o mishi,sai d'ai bai isa fidda ta cikin yawan
daliban ba. Washegari da safe a "area classis"
sai zancen jiyan ake, yana jin lokacin da aka ce
dayawa sunji ciwo,wasu na "dispensary ",kawai
sai ya samu kanshi da leka ajin su Fure,suma
d'ai maganar jiyan suke tayi,suna ganin shi suka
nutsu tare da g'yara zama. Juyawa yai,dan ganin
ba Fure a ajin,sai yai hanyar dispensaryn.
D'ang'walolo,tana k'wance sai wash! take tana
y'arfe hannu ana mata "dressing" d'in kafarta.
Murmushi yai, ganin dan ciwan amma take
wannan wash! d'in. Yana tsaye yaga an zaro
allura,Furen ya k'alla, ai kam ido ta zaro,"Allurar
mey za'a min? Tab! Baya ta ja kan ta mike tsaye,
"nifa na warke malam, na d'aina ma zazzabin,
mai allurar yace" kiyi hakuri kawai ki ju ya, dan
fa sai na miki. Kawai da mamakin shi yaga ta
6are baki tana kuka,kuma ba koh hawaye, dayar
y'ar "mate'' d'insu tace"haba Pretty,allurar? A
masife ta k'allo ta," eh din ina ruwan ki.
Murmushi yai,kan ya k'ada kai ya shiga cikin
"dispensaryn". By Feenat Ja'afar.
9/29/16, 2:15 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 6_Tana ganin shi ta
juyar da kai tare da d'aina kukan, ya koma gefen
da take, bata nufa ba taji yace "sannu Furera..
Da sauri ta dago,sam batai tsammanin bahaushe
ne ba, yafi mata kama da y'an chan kudu,fari
ne,dan sosai ya fita haske,mai sage siriri,da
tsayin shi,dan ya kere ta da kusan kai uku,da
gani mai hakuri ne, sai d'ai bai d'aukan raini.
Sosai yake da k'warjini, musamman agun y'an
mata. A hankali cikin sigar lallashi yace tai
hakuri a mata,kai ya k'auda, sai ta samu kanta
da d'an daga wa, gefen nashi yake take k'allo,
halamar bai son ganin abin,ido ta lumshe,lokacin
da taji tsinin allurar, "shikenan fa an gama, ido ta
bud'e, tare da sauke rigarta tana k'allon Uncle
Ahmad da har yanzu yaki k'allon ta, magani aka
zuba mata,dispensarern yace gobe ta dawo,
juyowa yai,lokacin da take k'ar6a. Tare suka
fito,tana d'an dingisa K'afa, shi kuma rike da
maganin da k'walin lemon da y'an k'wanarsu
suka kawo mata, mamakin ta yadda ya zamu mai
saukin kai,har aji ya rakata, a bak'in kofa ya
tsaya,tare da kiran Adama tazo ta k'ar6i kayan,
sudai y'an aji da ido suke binshi,sam ba wasa a
fuskar shi bare su tanka,tana zama ta k'allo shi,
hannu ya dago mata yana murmushi, itama sai ta
murmusa,baki sake suke k'allon su har ya juya
ya fita. Da sauri y'an class suka zo jin
gulma,wasu na Sonta yake Allah,harara ta basu,
"wani irin so? Ku fa baku kai. Ina,sukam y'an ajin
har aka tashi suna pretty ta uncle Ahmad. Tun
tana masifa har ta fara binsu da ido. Sai d'ai fa
ana zuwa bacci ta kasa sukuni, dan har yamma
sai da yazo duba ta,harda drinks d'inshi mai
sanyi da cake. Takan yawaita murmushi in ta
tuno shi,wanda ita kam a nata wayon bata san
meye ba.m Sai ya zamo Uncle Ahmad sun d'inke
da Fure sosai,d'uk da bai ce yana son nata
ba,asalima in yana " teaching'' yi yake kamar bai
san kowa ba a ajin,,dama kuma itace "class
captain" ta y'an iska,d'an ita d'uk randa akace ai
''noise maker" ranar take cewa kowa yai surutu
son rai,randa ba'a ce ai ba kuma zata chunkune
kaji aji tsit,tari kai sunan ka ya shiga. "Records"
na exams nasu suke su da uncle Ahmad, suna
karanto mishi ita da Adama,ga nan wata na musu
firfita,har Adama ta gama nata pretty ta fara.
Yadda take fidda lafazin cikin murya mai dad'in
sauraro kai kace tun daga "primary" ta samu
"good foundation'', sosai yake jin muryar ta har
tsakar kanshi, yakan rasa mey yake ji a game da
" pretty" in dai zai tsinkayi muryar ta. Jim
tai,yana jiran ta fad'i "next" tai murmushi,
"Furera muh'd, murmushi yai kan ta fad'a mishi
mark itama tana murmushin, Adama ta zunguri
mai firfita suna gulmar su. A zahiri kowa na son
kowa,amma sun kasa gano hakan,shi d'ai uncle
yasan yana yawan tunanin Pretty, amma sam bai
kawo so ba. K'wance tashi har sun kusa gama
service d'in su,a dalilin uncle Ahmad Fure ta
nutsu sosai,har d'aurin karatun addini yake musu
ita da K'awayenta,da nusar su yanzu sun girma
su daina kaza da kaza,,sosai kamar K'anwar shi
haka yake ji da ita,randa yai k'wanan waje in
bata ganshi ba d'uk sai taji kamar tana jin
zazzabi, d'uk a tunanin ta ba d'an KD bane. Ana
gobe zasu tafi lokacin su Fure na ss3,kuma "
Head girl" Duk tabi tai laushi, a kofar aji suke a
dandamalin a zaune, kowa ya zuba musu na
mujiya,k'allonta yake ba ko kiftawa, ita kam kai
d'uke kamar ta sau kuka, a dan karatun littafin
soyayyarta ta zata sonta uncle d'in yake,ashe ba
haka bane,gashi har yau zai tafi bai furta mata
ba. In d'ai batai k'arya ba ita kan tasan ta rufta a
son shi,murmushi yake,"Furera" kai ta dago,da
dan murmushi a fuskar ta,''ki kula sosai,kinga kun
fara "practical", kiyi karatu ko d'an ki fita da
result mai k'yau. Kai ta k'ada mishi, wayan shi
ne ya k'ada kirar" Blackberry" da murmushi ya
daga kan ya ambaci sunan "Mama" sai ya d'an
tashi ya matsa, sai da ya gama ya dawo
fuskarshi d'auke da murmushi, "Mama na gaida
Furera, murmushi tai kan ta k'ada kai," ina
amsawa. Har address d'in Fure ya k'ar6a, da
alkawarin zai kawo mata ziyara har gida in sun
gama makaranta. K'warai ta d'aure ganin batai
kuka a gaban shi ba, sai d'ai yana tafiya ta k'ar6i
"pass" tai ''Hostel". Kuka take wanda da
biyu,itama d'ai ta zurma d yawa, amma irin su
Uncle Ahmad tasan ba ajin su bane,wai k'warya
tabi k'warya, yadda yake da aji da k'yau tasan
yafi k'arfin ta, zuciya kawai ke yaudarar ta. Tun
tana damuwa da son Uncle Ahmad har ta jingine
shi ta hau karatun ta. In har da rabon zasu gana
kila ta ganshi. Sun gama "exams" kowa ya tafi
gida da k'ewar juna da dunbin k'yaututtukan
ta,sa6anin Adama da suke kusan unguwa d'aya
da Pretty. K'allon Fure Umman su take,d'uk ta
rame kibar nan ta dawo y'ar chas da ita,"har yau
ina mamakin ramar nan taki Furera,ko A'i batai
rabin ramarki ba data gama makaranta.
Murmushi tai,kan tace"Umma karatu ne, zai
maida kiba ta har da k'ari, kai ta k'ada, sai dai
har yau tana mamakin yadda Fure ta nutsu gaba
d'aya, ta zama wata irin sassanya,a zaton ta d'uk
makarantar ne, sai d'ai gashi har sun shafe wata
1 da gama makaranta Fure na yadda take,kawai
sai ta bada girma ne ya shigi Fure. Abu d'aya ke
ci mata tuwo a k'warya yadda shiru ba labarin
Uncle Ahmad, ga yadda tsabar tunanin shi ke
hanata sukuni,takanji zuciyarta na wani iri in ta
tuno shi, gashi ko numbern shi bata rike ba,
dabara ce ta fad'o mata,fatan ta Allah sa Abban
su yai saving numbern, dan tana yawaita kiran
shi da ita. By Feenat Ja'afar.
Like 路 2 路 Reply 路 Report 路 Apr 14
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 7_Da dare Abba ya
dawo a wajen aiki ta d'au wayan da nufin zata
kira k'awaye, d'akinsu ta kule,kan ta hau duba
"contact" "Fure schl" taga sunan wani contact,
tasan kenan numbern da take kiran Abba dashi
ne a makaranta, gabanta na fad'uwa tasa
numbern a "private" kan tai "dailing'' g'yara
k'wanciya tai,tana sauraron yadda wayan ke
"ringing" bugun zuciyarta na k'aruwa, sai da ta
kusa yankewa har ta sadddak'ar ta sinkayi
sallamar shi da muryar da ke sata cikin nutsuwa.
Ido ta lumshe tana sauke numfashi da sauri,
hannu tasa a d'ai-d'ai zuciyarta dake mata
barazanar fitowa fili. "Da wa nake magana pls?
Sai a sannan ta bud'e ido,tama manta da ya
d'auka,sai da ya kara sallama kamin a hankali ta
zare wayan a k'unnenta tana hawaye ta kashe.
"Ashe ita kad'ai ma ta damu dashi? Kila ma shi
ya manta kashin wata Fure a wani gu, zatan ta
baya ma kasar, dan yasha sanarta "England" zai
je masters, ashe yana kasar a garin amma bai ko
neme ta ba har tsawan wannan lokacin... "Fure
lafiya? Umma ce ta katse ta,da sauri ta goge
hawayen tare da k'ak'alo murmushi, "ba komai
Umma,, da mamaki Umman tace "ba komai ki ke
kuka? Jin dad'i komai? Kai ta k'ada,tare da
kawar da zancen da cewa "yaushe Aisha zata
dawo Umma? Zama Umman tai,kan tace" a satin
nan zaki ganta, ai tasha hutu kusan wata biyu
kenan,amma Furera tun dawowar ki na fuskanci
kin sauya, kin zama shiru-shiru, kodai ba ki lafiya
ne? Kai ta k'ada kan a hankali ta zame ta
k'wanta cinyar Umman, "Umma ba komai,
makaranta make ma son shiga Umma. Kai ta
k'ada mata," yana da k'yau, Allah shige
gaba,amma sai kin tsaida tunaninki waje d'aya,
gashi har yau kin kasa maida jikin ki,sai ma wata
ramar da naga kina yi. Kai ta k'ada mata,kan tai
ko'k'arin had'iye kukan ta. Gaba d'aya ta tattara
Uncle Ahmad ta jingine shi gefe,har numbern shi
ta ma goge,dan in d'ai ta motso mata in ba
muryar shi taji ba bata samun sa'ida, yanzu kam
Alhamdulillah, ta samu ta fara manta so,sai d'ai
"memoryn' baya yana a K'wak'walwar ta. Yanzu
karatun ta kawai tasa a gaba,a bangaren
''catering''. Yaya Suleiman ya kamalla karatun shi
har an bashi aiki,yanzu burin shi aure,sai dai har
yau bama budurwar,babban burinshi kamin na
yanzu bai wuce ya tara kud'i ya tada ginin Abban
shi ba,dan sosai yake da murad'in iyayenshi suyi
nasu su huta da haya. InshaAllahu zaya hutar da
Abba aikin makanikanci bada jimawa ba,yai
alkawarin ji da iyayen su da y'an uwanshi dad'i
na duniya in har Allah ya bud'a. Albashin shi na
farko Abba da Umma ya direwa,a ganinshi su yafi
kamata su fara ci kamin kanshi, musamman
Abban su mai arzikin zuci,ya sani da Abban su
mai jajircewa ne mai kuma nema da guminsa,shi
yasa yake kara alfari dashi yake kuma neman
koyi da dabi'un shi. Zaune suke da
yamma,dawowar shi a aiki kenan suna zaune a
katuwar darduma a tsakar gida shida Umma da
sauran k'annen shi,yakan yi nishadi in ya ji shi
cikin gida haka da d'uk Familyn shi,Abba kawai
ya rage baya a cikin su,tad'in bikin Aisha suke da
Umma, yayinda Fure ke zaune tana taya su
Hassan da Hussaini "Assignment",sai d'ai jefi-jefi
yayan nasu na sako ta cikin zancen. Ka gansu
g'wanin ban sha'awa, gidan su ba k'yara bare
hancini, kowa yana nan-nan da juna. Adama tai
sallama, cike da murnar ganin K'awarta ta shigo
gidan. Wani ihu da suka zuba kan Furen ta tashi
suka ruk'unk'umo juna, daga Umma har yayan
baki suka saka suna k'allon su,toh g'wara Umma
dama tasan halin Adama da Fure,amma shi da
mamaki kawai yake k'allon su musamman
Adama, sai da suka gama rawar kansu tukun
cikin kunya ta gaida Umma,kan ta sauke
k'allonta akan Ya Suleiman,da halamun kowa d'ai
yai katari da " soul mate " d'in shi, dan kasa tai
da kai,lokacin da ta gano waye shi,shikam
k'allonta kawai yake da murmushi,kai duk'e tace
"ina yini Ya Suleiman, Fure ce ta katse shi,"
Adama ce fa Yaya,ta girma koh? Murmushi yai
kan ya amsa,"ai sam ban gane Adama
ba,"2years" d'uk sun kara girma,koh Umma?
Murmushi ita d'ai Umma tai,da halamun ta gano
bak'in zaren. By Feenat Ja'afar.
Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 Apr 14
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 8_D'aki suka shige,
suna firar yaushe gamo, "kawai ki kaje kikai
zamanki a Abuja abinki? Murmushi tai, kan ta
ware "pashminan" kanta, "k'awata Abuja tayi a
rayuwa, ke! Bari kawai, Allah kamar kar na dawo,
naci fa na k'wanta, hatta kayana wanken ake.
Hannu ta bata suka tafa tana "shege Ada,kinyi
k'yau ke kin ganki? " ke d'ai bari, zama ta g'yara,
"kai k'awata yayan kun nan fa Allah sai had'uwa
yake kara yi, d'uk yafi y'an gidan nan k'yau fa..
Dariya ta tuntsire mata dashi, kan ta bata suka
tafa, " dad'ina da k'awata ba fulako,ki ce munyi
kasuwa? Hannu ta kai bak'inta halamar tai a
hankali,"Allah dama ranar yace nai mishi
budurwa a unguwar nan,sai kuma naga shima
kamar ya zurma. Wasa-wasa d'ai zance ya
tabbata tsakanin Adama da Ya Suleiman, har
magana taje gidan su Ada, sosai ba wanda yakai
Fure son wannan had'i, sai kuma su da suka
k'ulla abunsu. Biki kam ya karato, d'uk da yazo a
lokacin da Fure ke shirin y'in Exams a school.
Tafe suke ita da Aisha da k'awayenta su biyu
daga saloon,ganan g'wagg'waran su a leda da
aka nad'a musu, k'awayen suka tsaida 'Taxi"
suna sanar da Aisha sai goben, sauri suke, ganan
magriba ta wuce amma hanya d'uk "go slow", sai
sunyi kamar zasu t'sallaka sai Fure ta
r'unkumota har wata motar ta taho, t'saki Aisha
tai," wallahi kamar tashin k'auye kekam, da tuni
mun wuce sai wani rirrike ni kike. "A ke,rai d'aya
ne, a yadda kowa yake saurin nan muje wucewa
da garaje kawai sui ciki damu? Kai Aisha Amarya
ta k'ada," toh ni kam zan t'sallaka, dan kinsan
Abba in ya dawo ya tarar bamu dawo ba fad'a
zai,in yaso randa mutane suka d'auke K'afa sai
kizo. Hijab d'inta ta rike,"wallahi baki isa ba.
Yanzun kam mota suna d'an nesa, hannun Furen
ta kama"ki biyo ni toh yanzun. Da d'an gudunta
Aisha tai gaba,sai jin Fure ta zame hannunta tai,
"tsaya ledar mu, ina, A'i har ta wuce,da sauri ta
ju ya da nifin ta t'sallaka t'saut'sayi, ashe wata
jar CRV ta kuts'o,da gani kuma sauri su ma suke,
gashi tazo t'sakiyar k'walta,ga ihun Aisha na tai
gudu ta karaso. Ga ihun "horn" din motar,d'uk sai
ta kasa gaba ta kasa baya,suka had'u da tsoron
k'walta suka rikita Fure,ido ta rintse,tare da
sakar ledar kayan a kasa ta rufe k'unnenta da
hannunta d'uk biyu, tasan ba makawa sai motar
nan tai ciki da ita. Jin shiru ba ai ciki da ita ba
saima hasken motar da ya dalle mata ido da dan
jin hayaniya yasa a hankali ta bud'e ido jiki na
ka'r-ka'rwa. "Da ke! ke da asara wallahi bamu
ba, so nai a yabimin ta kanki tunda kin gaji da
duniyar shi kuma ya tsaya.. Babbar mace ce,sai
d'ai da ka ganta zaka san isassiya ce mai ji da
kanta, k'allo d'aya zaka mata kasan naira na inda
take, fara ce mai kiba ba chan ba. Sam ita bama
ta lafiyar Furen take ba. Masifa take ma Fure
kamar ta rufeta da duka,gashi ita Furen ta tsaya
kem! Kamar an dasata a gun,har yanzu jikinta na
ka'r karwa, Aisha data karaso ita kad'ai ke bawa
Hajiyan hakuri,tare da ko'k'arin janye Fure. Wasu
da suka gaji suka zame bi ta gefe. Haka take ga
wanda yake " driving ",tunda ya taka birki yake
k'allon wacce yaso ya bige, kamar wani wawa ya
sau baki yana k'allon Fure ba ko kiftawa, ganin
suna neman tafiya yasa da sauri ya 6alle murfin
mota yai gunsu, Hajiyan ta zata k'addamar musu
zai yi sai taja baya,yace"Momy shiga mota in zo
yanzu. Sai da yaga ta shiga mota yai gunsu
Furen," Aisha. Da sauri Aisha ta dago,wanda
Fure itama tai saurin dagowa lokacin da zata
d'au ledar, "a pharmacy? Ba d'ai kai ne a motar
ba? Idon shi akan Fure yake yana murmushi,
yayin da itama Furen ta zuba mai ido ba koh
kiftawa. Tabbas itace,ya fad'a a zuciyar shi,sai
da Aisha ta kara magana kan ya juyo gare ta,
"kuyi hakuri amaryar mu,sam ban zata ku bane,
kan Fure ya dawo, " Furera da fatan bakiji ciwo
ba?....Momy ce ta katse shi da cewa "Kai dare
fa na kara mana a titi, kabar wannan yaran dama
y'an titin ne daga gani mu tafi. Wai waya wa
yai," toh Mom,coming. "Ku kara hakuri pls
Amarya, ya dubi Fure,da itama shi take k'allo ba
ko kiftawa, Aisha ma da mamakin ina yasan Fure
take, sai kuma mamakin uwar shi bala'e'iya,
Tana nan a haka har sukai sallama amma ita ta
kasa furta komai. Har ya shiga mota shima yana
waiwayen ta. Ko da suka je gida su Umma suna
ta tambayar su ina suka tsaya har haka? Furen
Aishan ta k'alla, "Umma amare ne sukai yawa a
garin,ga gidan mai kunshi ma acike. ''Toh ita
Furen mey ya same ta? Koh yunwar ce? Da sauri
Aisha ta k'ada kai, dan tasan in d'ai ta sanar da
Umma abinda ya faru yanzu zata rikice. Juyi
kawai take a katifa, har yanzun ta kasa
t'ant'ance murna take ko akasin haka? Ga Aisha
ta dameta da tambayar ina Ahmad yasan ta? Kai
kawai ta k'ada mata, kan tace itama bata sani
ba. Juyi ta kara yi,sai ga hawayen da tun dazu
take bidar su zubo sunki sai yanzun. "Dama
uncle Ahmad na garin nan har yanzu? Lalle
yanzu ta kara tabbatar da ihu kawai take bayan
hari, tunda har address ta bashi in yaso zai neme
ta. Haka ta lulluba tai mai isarta kan ta sa a
ranta indai tana da zuciya toh tabar tuna uncle
Ahmad. Suma chan su Momy tun a mota take ta
kara zagin su Fure,shi d'ai yai shiru,tunani ne fal
ranshi har suka zo gida. K'wance yake yana
k'allon" A.Cn d'akin nashi, kawai yanayin Fure
yake tuno wa, ashe Allah zai sa yaga Fure a
fad'in garin nan bayan rasa address d'inta da
wayar shi? Murmushi yai,a hankali ya
furta"Pretty" sai kuma ya gintse. Tabbas Fure na
matukar kama da Aisha,sannan sosai yasan
yayan Aishan a A.B.U,toh meye had'in su da
Fure? Dan tun dawowar Suleiman a dalilin auren
Aisha sau biyu yana zuwa gidan su,amma bai
ta6a ganin Fure ba... Gaban shi ne ya fad'i
sakamakon tunawa da zanchan su na jiya da
Suleiman d'in, kan wacce zai aura makarantar da
yai service tayi,kuma shekarun d'aya.. Kar fa ace
Furera ce wacca Suleiman zai aura? Kila koh
y'an uwa ne shi yasa suke kama... Cewar wata
zuciyar. Tashi yai zaune,dan tuno da g'yaran
amaren da suka sha ga uban lalle da kayan
g'wag'gwaro da suka fad'i kasa. By Feenat
Ja'afar. 庐NWA. Feenat.mywapblog.com
9/29/16, 2:17 AM - Queen Safiyyert馃憫: [4/16, 12:30 PM] Feenat Ja'afar: "JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
9_Washegari "10am" a kofar gidan su Aisha ta
mai,a kofa ya same su, da halamun daga wani
waje suka dawo,tsaye suke da Ya Suleiman suna
ta nishadin su da dariya,tun a nesa kawai ya
bada hasashen shi ya zama gaskiya,toh amma
ita Furen wace tasu? Ina ne gidan su?
Tun tsayuwar shi Fure ta tsagaita dariyarta tana
dub'en motar,tabbas ta jiya ce, k'allonta Yayan
nasu yai,kan ya k'alli inda take k'allo, tuni fara'ar
shi ta karu tare da furta"A'a, AAA.. Kan yai
wajen shi,Aisha ma ta fara fara'a, ita kam kasa
tai da kai,dan ganin suna yin wajen su da Uncle
Ahmad d'in.
Idon shi na kanta,ganin yadda Yayan nasu ya
shiga t'sakiyar su ita da Aisha,da fara'a suka
gaisa da Aishan,kan itama tace"Uncle ina
k'wana.. Damm! Ya ji zuciyar shi ta buga,a
hankali ya amsa,tare da d'auke kai a kanta,
shikenan Pretty ta fita a rabon shi? Ido ya dan
rintse,"kai zurfin ciki bai ba a rayuwa, gashi yana
k'allo k'wado zai mishi K'afa.
Ya Suleiman ya k'allo shi, "nasan dama zaka
sansu, sai ya k'allo Fure da murmushi, itama ta
k'akalo murmushin dole. "she's my.. Da sauri ya
tare mashi numfashi da fad'in" I know, sai yai
murmushi a takaice, kan ya k'allo Furen, Ya
Suleiman yace"ok,kun ta6a had'uwa a gidan ne
hala? Kai ya k'ada, duk sai ya ji tsayuwar ta
gundure shi,Aisha ce ta katse shi da fad'in
"Ina Angon ka barmin shi? sai kuma ta rufe fuska
ganin yadda Yayan su ya kafa mata ido, " iyee!
Lalle fitsaru. Shikam murmushi yai kan
yace"yana a masaukin shi,zai zo bada jumawa
ba.
"Zan wuce, dama Ilyass ne yace na tabbatar da
lafiyar Madam d'in shi,sai mun had'u a " Dinner ".
K'allo su Fure yai,"toh amare zan wuce,sai mun
had'u anjima, kai Fure ta k'ada mishi, kan ta d'au
ledar su ta shige gida,da tsabar takaici,ashe ma
ba dan ita yazo ba? Ajiye dilkar tai da suka
k'ar6o, tai ciki ta bar y'an biki a t'sakar gida.
Shikam a mota d'uk ya rasa sukuni, Fure ita ce
mace ta farko da ya fara jin " feeling'' akanta,
hatta Maman shi tasan da zancen Furera,yau da
ya sanarta yaga Furera k'warai ta tayashi
murna,har yaje gida sukuku yake jin kanshi. Sam
baida kuzari.
D'akin Maman shi ya zu6e, wanda indai maganar
mace ne toh dole sai wajen ta,amma sauran
lamari Momy ce ja gaba sama da Maman tashi.
Mata biyu ne ga Baban shi, Momy itace Uwar
gida,yayinda Mama ke amarya, d'uk a zankuwa
aka haife su, sai d'ai lokacin su Ahmad na yara,
kamin suka dawo Kaduna da zama gaba d'aya.
Baban su Alhaji Abba Ahmad "costom" ne kan
yai "resining" ya zama d'an k'wangila.
Sosai yana da kud'i, sannan da dattako, Momy
nada fad'a, sam taki jinin talaka,dan baban ta
babban "costom" ne lokacin da Alhaji Abba ya
aure ta.
Ga matukar dagawa da raina mutum,ga son fasa
taro,komai ita ke ju ya shi son ranta a
gidan,yaranta 3,Hauwa(Aunty Jidda), itace babba
a gidan,sai Nasir,da Huwaila, sai y'ar K'anwar ta
da take ruko Rukayya.
Kan aka auro Mama, d'uk itama gidan su ba
laifi,gata mace ce har mace,mai hakuri da
t'sabar sanin ya kamata,tana da kawaici, kullum
zaka samu fara'a k'wance kan fuskarta, da fari
Momy ba taso zama da kishiya ba sam ita,
sai d'ai kuma wani had'in Allah, kawai sai tasu
tazo d'aya, dan komai ta sakar mata ta
mallake,hatta yara in ta haifa toh sun koma
zaman d'akin Momy,ita kam dake mai hakuri
ce,d'uk sai ta sallama mata su, yaranta
shida,Usman, wanda shine mijin Aunty A'i, sai
Aunty Maryam,Ahmad,da Ummi autar ta rasu.
Amma d'aya kawai ta rike wato Ummi.
T'sakaninta da sauran sai gaisuwa koh in taje
bangaren Momyn,sai ko randa ta motso musu
suzo bangaren ta,dan ita k'wa6arsu take matuka,
amma a d'akin Momy sunan ka"kai komai ba
komai na".
D'uk da mugun hali irin na Momy sam batai ma
yaran Mama mugunta,batta da mitar ta,hakan ne
yasa ita maman sam bata damuwa,sai d'ai abu
d'aya, duk yaran kad'an ne basu kin talaka da
raini,wannan dabi'ar ita kad'ai ke ciwa Mama
tuwo a k'warya.
Dan tamkar fad'an Allah d'uk yaran gidan sai mai
kud'i, in maza ne sai ya'yan manya masu k'yau.
Hudubar Momy kam tai aiki,Ahmad shine ya fita
daban,wanda sam baiya burin auran y'ar masu
dashi,sannan kuma k'yak'yawa.
Asali ma tun tashin Rukayya Momy tace itace
Matarshi, shikam fur yaki, dan ka'f ba abinda ta
bari a halin Momy,tamkar ita ta haifo ta.
Gadai k'yau har k'yau, amma sam ba hali. Shi
yasa ko dariya Ahmad bayayi a gaban ta,
asalima ita d'uk gidan shi tafi tsoro.
Takanyi ma Momy kukan sam Ahmad bai kula
ta,sannan ga hancinin tsiya. Momyn takance ta
k'wantar da hankalinta,Ahmad kamar ya zama
nata an gama.
Haka kowa yana da burin fita kasar waje yai
karatu a gidan amma banda Ahmad.
Rayuwa mai sauki shi ya za6arwa kanshi, kuma
a zahiri kowa a gidan naji da Ahmad, har sukan
kira shi da mai "ra'ayin kanshi".
Anan ya had'u da Ilyasa,yayinda shi Ilyass yake
abokin Ya Suleiman. Nan suka k'ulla abota, duk
da kowa bangaren shi daban,sannan ba yadda za
ai ya nuna maka shi d'an wani ne,dan ko mota
bai ya zuwa da ita cikin A.B.U.
Ko Abban ne a yanzu d'ai da Ahmad yake yawo
ko ina zashi,tunda sauran manyan yaran kowa ya
kafu da K'afarshi.
Sosai Abban su yake son yaran shi,haka bai son
takura musu,yai musu sa6o da jin dadi,d'uk da
shi d'ai bai kin talaka,sannan baida wulakanci.
Mama ce ta k'allo Ahmad," ya d'ai? Har ka dawo
a gun Fureran? Kawai sai ya k'wanto cinyarta
"Mama aure zatai go6e.." Ya Salam! Shine
kalmar da maman ta fad'a.
Kamar ya k'urma ihu haka yake ji.
"Ita ta fad'a maka? Kai ya girgiza, " A'a, Aboki na
d'ai zata aura.
Kanshi ta shafa cikin sigar lallashi, "kai hakuri
toh,Allah yasa hakan shi yafi zama alkairi, Amma
sosai nima d'uk da banga Furan nan ba ta shiga
raina. Nan tai ta bashi baki,kan matar mutum
kabarin shi.
By
Feenat Ja'afar.
[4/16, 1:44 PM] Feenat Ja'afar: "JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
10_Da k'yar ya iya shirya wa zuwa wajen
"Dinner". Sosai yai k'yau cikin manyan kaya yau
da ya shige su,dan shi ma'abocin kanana ne.
Farar shaddar ta matukar k'ar6ar shi, ga hular
nan ta kama,sai kamshi yake kamar Angon ba
wai abokin Angon ba.
Parlourn Momy ya shiga,don sanarta ya fita.
Rukayya ce kawai a parlourn tai d'ai-d'ai a kujera
tana " 2go". Tana ganin shi ta mike da rawar kai
harda ce mishi yai k'yau, baki ya d'an ta6e kan
ya had'e rai''ina Momy? Da dan harara ta nuna
mishi d'aki ta koma ta k'wanta a ranta tana"ka'r-
ka'ra a d'aura mana aure ne,zaka shigo hannu.
Sukuku ta gama shiri tun jiya batta kuzari,
hakanne ma yasa Y'an uwan suke d'an sata
nishadi,amma da anjima zata dawo gidan jiya,su
sun d'auka koh rabuwa da Aisha ke sata haka.
Tsaye suke a gaban madubin su na katako a
d'akin su,kanta kawai take k'allo, matuka tai
k'yau tamkar wata k'yak'yawar. Tabbas in kana
da k'yau ance ka kara da wanka.
A d'uk k'walliyar k'ewayen idonta yafi ko'ina
d'aukar hankali.
Ma'abociyar ita gashin ido ce dana gira sune
tushen k'yanta. Yau sunsha" Mascara'' da "eye
liner''. G'yaran jikin da fatarta ta samu ita ta
fidda ta zama " Black Beauty",
net ne "gown" "combination" d'in fari da "pink" a
jikin ta.
Daga sama aka sa farin zuwa chan g'wiwa,
kasan aka mishi tattara da "pink" d'in, da "head'
na "pink" da k'yali-k'yallin "silver''.
sosai tai k'yau ainun kamar itace amaryar.
d'uk da su masu karamin k'arfi ne amma ak'wai
zuciyar yi,dan sosai sun fitar da kansu
kunya,d'ai-d'ai g'warg'wadon hali Abba da Ya
Suleiman sun fitar su kunya.
Kawun su na Zaria shi ya d'au nauyin gado da
kujerun Aisha y'an zamani,sosai y'an uwa ma
sun musu kara abin sai son barka.
Adama ma tasha lefe Ya Suleiman kamar ba
go6e,ranar albashi yai rana da taimakon
makanikancin.
Aisha ce ta shigo ita ma sanye da" net"
"brown".. Sosai tafi Fure k'yau,amma a yau d'uk
sun had'u sunyi k'yau sosai.
Gaban madubin taje tana murmushi, kanta ta
d'aura akan kafad'un Furen, " y'ar uwa tamkar
kece amaryar kinyi k'yau ainun,, murmushi Fure
tai d'uk tai laushi, "ku nake tayawa k'yau tunda
kunyi k'yau kuma. Tai murmushi, "dan Allah
Furare mey ke damun ki? Tun randa abin nan ya
faru d'uk kin dawo wata iri, kinyi sanyi sosai,
"dazun naji kince ma "pharmacy" Uncle, amma
kince min baki sanshi ba,bayan Ya Suleiman yace
anan yai "service'' a school d'inku,mey kike 6oye
min ne? Murmushi tai kad'an kan ta juyo, gaskiya
ta fad'a mata kan ta sanshi sosai.
Ido kawai ya zubawa kofar " Hall" d'in dan jin
ana sowar ga Amare nan, Asha da Angonta ne a
gaba,sai gata ita da Ya Suleiman, sai dai shi ya
ju ya waje lokacin da ya gane Adama ta tsaya.
Ido ya rintse dan ganin lokacin da Ya Suleiman
ya rad'a ma Furen wani abu tana d'an tushe baki
da dariya. Tsayawa su Aishan sukai,har ta
karaso bai daga kanshi ba.
Tana daga kanta tai ar'ba dashi ido rufe,da sauri
ta d'auke kanta jin wani abu na taso mata a
zuciya wanda tuni ta rufe bab'in shi.
Sowar daya kara ji ne yasa ya bud'e ido,sai ga
Adama sun shigo da Ya Suleiman, da sauri ya
k'alli wajen su Aisha yaga Furen na tsaye tana
d'an murmushi tare da d'an had'a hannu tana
musu tafi a hankali.
Wata ajiyar zuciya ya saki tare da sakar
murmushin farin ciki.
"Dama Adama ce matar Eng.Suleiman? Kai
amma ansha dashi k'warai. Tashi yai Shima yana
d'an tafa musu da murmushi a fuska,kan a
hankali ya ju ya ga Fure, wacce itama da sa'a ta
k'allo shi,murmushi ta sakar mishi wanda kamar
dak'yar ya fito,kan ta d'auke kai a hankali.
Sosai ya famo mata wani ciwo,ga wani uban
k'yau da ya mata cikin manyan kaya yau d'aya,
dak'yar ta saita kanta.
Chan inda aka warewa abokan Ango da na Amare
ta nufa kai d'uke, kujerar da ke k'allon shi kawai
ta rage" empty " shikam har yanzun k'allonta
yake har ta zauna.
Ana gabatar da abubuwa shikam Fure kawai ya
zubawa na mujiya,sosai tai mishi k'yaun ban
mamaki, ga wata nutsuwa da yaga tai bala'in
mishi, kamar ba Fureran da ya sani ba. Kowa ya
tashi,na taka rawa suna yi,na yawo nayi, sai ya
rage daga Fure sai Uncle Ahmad.
Kai duk'e ta gaida shi da sanyin murya,jin bai
amsa ba yasa ta dago,murmushi yake yayin da
idon shi ke k'anta. Sai ta samu kanta da kunyar
shi.
Da k'yar ta samu ta zame da wayyon Adama na
kiranta.
Binta yai da k'allo, yau d'aya Fure ta kara
mamaye zuciyarshi, bazai kuma kara sakacin ta
ku6uce mishi ba. Wa yaga "real Love'.
Daga ita har shi har aka tashi fara'a suke, ita
kam batasan tata ta meye ba.
Maimakon yadda suka zo su koma tare ita da
Amare,kawai sai mazajen su suka d'auke su,Ya
Suleiman yace ya had'a mishi da y'ar K'anwar
shi da wata cousin nasu.
Ba dan taso ba suka shiga motar,wata "civic"
baka mai k'yau.
Baya Sadiya tai saurin shiga,wai ita ta shiga
gaban. Haka tai sakare,kan ta bud'e ta shiga,ya
ja su.
A hankali yake tuki cikin nishad'i,ya kan d'an
k'allota kad'an kan yai murmushi, itama takan
d'an satar k'allon shi ta gefen ido, fuskarta
sake,sai d'ai ba walwala,kowa y kasa ce wa
kowa uffan.
"A.C ya kara,kan ya hankali ya kai hannu ya
k'unna wakar da in d'ai zai ji ta toh Fure ke fad'o
mishi, sai d'ai yau gata gare shi, a hankali ya d'au
"remote" ya d'anna "play" sai ga nan wakar
"Nothing gonna change my love you ta shigo.
Tsam ta nutsu, tare da sauraran b'aitin cikin
wakar,sai ta samu kanta da lumshe ido kamar
mai bacci,tare da jingina kai a kujerar motar.
k'allo ta yai,kan shima ya jingina a kujerar yana
tukin shi cikin nishad'i,tamkar ance an bashi
Fure.
By
Feenat Ja'afar.
9/29/16, 2:18 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 11_Ido rufe kamar mai
bacci taji sun tsaya,maganar sadiya ta tsinkaya
tana mishi godiya,kan ta fita,k'allo shi tai,kan
cikin sanyin murya tace"mun gode Uncle, ba ta
jira mey zai ce ba ta fara ko'k'arin fita,sai dai
gam, kofar a kule,tsam tai,kan a hankali ta juyo
ta k'alleshi da halamar tambaya. Shima idon ya
zuba ma ta,sai ita ta k'au da nata,kusan minti
uku ya ki magana, ita kuma tsabar haushin shi
ma take ji,wanda ita kanta bazata ce ga dalili ba.
Chan yai ajiyar zuciya, kan cikin nutsuwa
yace"Furera... Kanta na gefe ta amsa,sai kuma
ya kasa ce mata komai,mota ce ta hasko su,su
Aisha ne, gaba d'aya suka bisu da k'allo ganin
yadda suke a nishad'i, kawai sai ya d'anna
"unlock" kan yace"ki tsimaye ni gobe..dan
K'allonshi tai kan ta k'ada kai tai waje,da k'allo
ya bi ta, kan shima ya fito. Gun su Aisha tai,duk
jikinta yai lak'was,ganin ba Adama tasan sun
kaita gida. T'sakiyar su Ya Suleiman ta shiga da
Aisha, yayansu mai saukin kai ne,ba ruwan shi
da hantarar su ko k'yara, shi yasa k'warai ya
zama abokinsu. Murmushi kawai Ilyas yake
musu,ganin yadda Fure ke shag'wabe fuskarta.
Uncle Ahmad ya karaso yaga Ya Suleiman ya
kama hannun Fure,sai ya t'sinkayi maganar shi
cikin lallami,"wai Aisha mey ya samu Furii ne tun
jiya bata da walwala? Murmushi tai,kan ta k'alli
Uncle Ahmad wanda idonshi ke kan Ya Suleiman
a na Fure. "Na tambaye ta tace ba komai. Ilyas
yai murmushi," hala bata son ku tafi ku batta ne?
Gida su Aishan suka shiga,kan su kuma suka hau
fira a kofar gidan. Kasa d'aurewa Ahmad yai,"wai
ni Engnr. Meye had'in ku da Furera pls? Na kasa
gane wa fa.. Dariya sosai Ya Suleiman shida
Ilyass suka,kawai sai ya sa musu ido,shi d'ai
amsa yake nema. "Amma tambayar ta ban
mamaki "pharmacy", cos jiya ka ce min" you
know'' I thought ko a makarantar su kasan ta ai.
Kai ya k'ada, "Eh,amma bansan nan ne gidan sun
ba. Ilyass ne ya dafa shi da d'an dariyar shi,
"kana da abun dariya Aboki,hala neman iri ka ke
ka fara bamu girma tun yanzun? Murmushi yai,
tare da k'ada mishi kai, " toh abinda yai Aisha
shi yai Fure yai kuma Engineer.." Same Ma,
same Baba.. "Ko in ma ta d'an g'wari-g'wari? Kai
ya k'ada murna fal cikin shi,kan ya k'allo
Suleiman, wanda har yanzu yake dariya kasa-
kasa. " a gaskiya na wahala a neman K'anwar ka
Engr. Ashe tana a kusa ma ban sani ba?
Murmushi yai, kan ya k'ada kai. "Pretty".....
"Furera''.... Kai, yanzu na gane, ashe ita ce
wacce ake neman nan ido bud'e. Cewar Ilyass
cikin shakiyanci. "Shegen kaya, kai yanzu ko
kamar ai zaka d'akko hanya. Kai ya k'ada yana
murmushi, kan yace "a bar zancen kawai, amma
ni kam,naga gida. Dariya Ilyass ya sa
mishi,shikam Suleiman k'ada kai yai, dan sosai
yasan had'in yayi, lalle k'annen shi sun dace da
mazajen aure na k'warai. Dan Ilyass abokinshi ne
sosai,tun a Zaria, ta dalilin shi yaga Aisha,
sannan yasan Ahmad, sosai ya yaba da yadda
yaje gidan su Ahmad yasha k'allo, amma sam shi
bai ta6a nuna musu shi d'an wani bane. Kai ya
k'ada, yana mai adu'ar Allah sanya alkairi. Bak'in
nan kamar gonar audiga ya shiga gida," direct "
d'akin mama ya nufa,suna parlour ita da Ummi
suna k'allo, yadda yake fara'a ne yasa mama
K'allonshi itama d'auke da tata. "Ka dawo? Kai
ya k'ada, kan ya k'alli Ummi wacce tai likwas
cinyar Maman tana mishi sannu. Da murmushi
yace "Je kice Momy na dawo a kai min abinci
d'aki.. Kai ta kada kan ta d'au dank'wali ta yafa,
kusan Ummi halinsu d'aya da Ahmad, shi yasa
tasu tazo d'aya, dan rainon mama ce ita. Tana
fita ya k'allo mama. "Mama pretty ashe K'anwar
Suleiman ce uwa d'aya, ashe ni ne ban gane ba
sai yau. By Feenat Ja'afar.
Like 路 Reply 路 Report 路 Apr 18
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 12_"mashaAllah, ashe
Furera na kusan mu ma. Kai yai kasa dashi yana
dan sosa keya yana murmushi, mama tace"toh
Allah sanya alkairin shi,sai d'ai bansan yadda
zaka kaya da Momyn ku ba Ahmad? K'allota
yai,kan yace"gaskiya mama Rukayya bata a
matan aure na,cos ba lalle muyi zaman aminci da
ita ba nasan. Kai ta k'ada, lalle tasan ak'wai
rigima a kasa,dan sarai tasan yadda Momy ta
d'aukaki had'in nan nasu Ahmad da Rukayya, ita
d'ai tasan nata ido, sai kuma tabi su da adu'a.
Washegari "10am" aka d'aura auren masoyan
biyu,basu samu kansu ba sai dare bayan ankai
amare gidajen su,d'uk anan suke. Shi yau ma ya
d'akko ta daga gidan amarya,yau da ita da autar
su,cikin nutsuwa yake sauraran surutun
Amal,bata fi "4yrs" ba, kawai sai ya ji babyn ta
shiga ranshi, sosai tana mishi kama da Furen shi.
Kawai sai ya fara bata tad'in Fure a schl. K'allo
ta yai,itama fara'ar take,sai yai murmushi, Amal
tace "Uncle, kuma kana d'ukan Aunty Fure in tai
surutu a class irin Uncle John? Harara Fure ta ju
ya ta sau ma ta jin tace mata Fure. Murmushi
yai lokacin da suka had'a ido da Furen. Kan yace
wa Amal "nop,sai d'ai na sa ta " kneeling" dan
kinga ai ta girma koh? Kai ta k'ada mishi tana ma
Furen dariya. "Toh kuma tana kuka? Sai ya k'alli
hanya yana tuno wani lokaci a baya.. Akan Fure
ya sauke idon shi, wanda take k'allon titi ta kasa
k'unne ta ji amsar shi. Sai yai murmushi, tare da
k'ada ma Amal kai, "sosai,har tana kiran Umma
tazo ta taimake ta.. Dariya suke mata, ita kam
kai ta lang'wa6e mishi, " kai Uncle A,ni d'in? Gira
ya daga mata,sai kuma ta d'auke kai. G'walo
Amal ta mata tana "woo Aunty Fure.. A karo na
biyu tace"wai waye Fure? Dariya yai har da
d'ukan sititari,ganin yadda tai da baki gefe Amal
ma ta mata. Yace!" No Amal,daga yau sunan
ta"Aunty Pretty... Baki suka saka,ita na
K'allonshi, Amal na k'allonta. Ido ya k'anne
mata,da sauri sai ta d'auke kai tana murmushi,ya
akai yasan Pretty? Ko a schl? Amal tace,"La!
Uncle "Pretty Zinta ta Jaduu? Dariya suka sa
mata d'uk, kai Amal. Haka har suka zo gida Amal
na musu abin dariya. Tsaida mota yai,kan suka
fito,ganan y'an kai amare wasu suna waje,sai
Amal tai gida wai d'akko mishi "sweet". Da k'allo
ya bita, har ta shige gida kan ya dawo kan Fure.
" pretty"...Buguwar zuciyarta ne ya dawo take
yau,dan jin ya ambaci sunan ta cikin sanyi, a
hankali ta amsa, "Ashe Engr. Yayanki ne? Kai ta
daga mishi,kan a hankali tace" Umm. "Sai ki ka ji
ni shiru ba? Kai ta duk'ar, ba tare da tace kom
ba. Tsayuwa ya g'yara, kan ya fara bata labarin
bayan rabuwa. " A motar haya na gamu da mai
yankan aljihu,waya na da "Address" naki da na sa
d'uk ya de6e, k'warai na fi jin ciwan 6atan
"address" d'inki sama da "phone'' na,karshe nai
"losing" "contact " na Abba,ko da nai "swapping"
still ban samu ba..kai ta dago,da mamaki ta
k'alleshi. " kin san dalili? Kai ta k'ada. Amal ce
ta dawo da alewa a leda tana bashi,sai yai
murmushi, maganar da bai gama mata ba ya bari
kan sai gobe sa had'u, ya kuma nemi number, ba
musu ta fad'a mishi. Sukai sallama Amal na
mishi "bye-bye. Tun da yazo k'wanciya zaro
wayanshi yana duba pic d'in da mai " photo" ya
tura mishi na pretty a waya. D'uk da halamun
bata ma san an d'auka ba, dan sam ba ta da wal
wala sosai,sai ya bada "style", sosai ranar ta
mishi k'yau, shi yasa yace mai hoto d'uk
motsinta ya d'aukar mishi ita. Murmushi yai tare
da shafo wanda takewa Adama murmushi, a
hankali ya furta "Furii pretty". Kawai sai ya raya
ya kira ta ya ji muryarta ko zai samu na bacci.
"Tea" take sha lokacin taga wayanta na d'an wal-
wal. Kofin ta sauke,kan ta kai hannu ta daga,
wayan ta kurawa ido, tasan numbern,sai d'ai ta
k'wanta mata. Saura kad'an ta kat'se ta
daga,shiru tai dan jin ko wacce take zargi
ce.."Assalam Alaiki Furiii...Ido ta lumshe, tare da
saita kanta da sauri,dan har ranta taji sunan,d'uk
da ta gane mai maganar, sai ta basar,''walaikum
salam.. Daga chan yai ajiyar zuciya, muryar Fure
na daga abinda yake son ji a tare da ita.. "Hope
kin gane mey magana? Kamar ta ce" eh, sai kum
tace, "ban gane ba kam.. Murmushi yai, kan ya ju
ya tare da rage karar *TV".Yace "coper Ahmad
Abba Ahmad, (AAA) " Chemistry " "teacher''..
Murmushi tai mai sauti,wanda har ya ji, sosai yau
tana a farin ciki,, cikin nutsuwa da wannan murya
ta pretty kad'ai tace" am sorry Uncle AAA,I
thought koh... Sai kuma tai shiru. Tashi yai
zaune, kan yace"koh wa? Kai ta k'ada, tare da
k'allon sadiya da tai mata kurii da ido. "Ba kowa.
"ka je lafiya? Ajiyar zuciya yai,kan yace"lafiya
lau,ina Amal? Ido ta lumshe, sautin shi na neman
zarar ta,a hankali tace "tana gun Mama. Fira ya
cigaba da mata,kan yai mata sallama kan ta
tsimaye shi zai zo mata da batu in y'an biki sun
watse har gida. By Feenat Ja'afar. 庐NWA.
Feenat.mywapblog.com
9/29/16, 2:20 AM - Queen Safiyyert馃憫: [4/19, 8:11 AM] Feenat Ja'afar 馃鉁嶐煆� :
"JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
13_Wayan take k'allo, sai ta samu kanta da
murmushi, ji tai gaba d'aya ya wanke kanshi a
gunta,tuni taji wani sabon lamarin da yafi na da,a
hankali ta zame ta d'aura kai kan "pillow" tare da
tariyo had'uwar su zuwa yau, fatan yasa yazo
mata da abu mai dad'i.
Da tunanin juna suka k'wanta, shi kam harda
mafarkin "FURIIN" shi.
Washegari suna t'sakar gida da sauran bak'in da
basu tafi Ang'waye sukai sallama,anzo gaisuwar
sirikai. Amal aka ce ta leka,sai gata da gudu tana
rad'a ma Fure"Aunty Furera Uncle... Murmushi
tai,kan ta k'alli kofa, Ya Suleiman ne ya shigo,
tare da sanar da su Umman,darduma suka sa
musu,kan tace ya shigo dasu.
Chan bak'in kofa ta zauna,har suka shigo, tana
jin lokacin da suka gama gaisa wa Ilyass na
tambayar ta.
Leko da kai tai kad'an,d'uk sai wani sunne kai
suke har mutumin ta,d'uk da yana d'an wayancen
dagowa neman ta. A hankali tace musu
"Ina k'wanan ku... Cikin nutsuwa ya dago kai
zuwa bak'in kofar da ya jita, ido suka had'a, da
murmushi tai kasa da kai suka amsa.
Amal kam tana manne da Ahmad,wanda
murmushi yake saka in sun had'a ido da
Fure,cikin kunyar k'allon d yake mata ta buya
d'aki. Har suka zo fita yana d'an leken ya ganta
amma ba hali.
A zaure ya tsaya bayan sun fito,dan gidan su
Adama suka fara zuwa.
Amal ya aika wai ta kira mishi Aunty Pretty, da
d'an dariyar ta ta tafi kiran.
Jim tai kad'an, kan tai murmushi ta tashi,zani ta
sauya,ta cire hijab d'in jikinta,sai ta samu kanta
da t'sayawa gaban mirror, gashinta ta g'yara, ta
d'aure shi t'sakiya da k'yau kan ta sa hijab akai
ba dank'wali. Gun Umma taje,tace ana kiranta.
A zauren ta same su shi da Amal yana rike da
hannunta tana mai wai karatun ta na islamiya"
Asma'uillahi Husna".
Kai ya dago da ya sauke su kanta lokacin da
take musu sallama. Murmushi ya sakar mata kan
ya amsa,yau kawai kunya ce tazo mata tashi.
Shikam k'yau ta mishi a hakan ma da ba make-
up, a chan kasa yake k'allonta, wanda tuni ya
kara mata wata kunyar. Rabin tad'in nasu da
Amal su ke,kan ya tambaye ta yaushe zata
Aisha,tai jim,yau kam ta gaji,tun dazu take mata
nacin tazo ta riga tace sai gobe, ga d'ai bak'i
zasu zo, "gobe InshaAllah.
Zauren ya k'alla, na kasa ne amma wata iska
yake ji mai sanyin dad'i, ji yake kamar yace ta
shimfida mishi taburma kawai ya zauna suyi ta
tad'in su yana shan iskar zaure.
Tabbas yana alfari da Suleiman da k'annen
shi,har ma da iyayen su,rayuwa suke cikin sauki
da rufin asiri,ga kowa ka gani a gidan mai fara'a
ne. Sannan basu raina kansu wai dan wani ya fi
su,shi yasa sosai ya fara abota da Suleiman a
dalilin Ilyass abokin shi. Sai yaji ya kara son
had'a jini dasu,
Kai ya k'ada yace "Allah ta kaimu,,a hankali
tace"Amin. Ya Suleiman ne ya shigo zauren shi
da Ilyass yana ta dariyar keta, shi kam Ya
Suleiman murmushi kawai yake, gaishe su ta
kara yi,tana tambayar ina K'awar ta? Sai yai
murmushi, kan yace tana gaishe ta.
Sosai suke bawa su Ahmad sha'awa ganin yadda
yake ji da y'an k'annen shi. Janshi Ilyass yai
yana mishi tsiya sukai waje,sai ya juyo tare da
kai hannu k'unnenshi a hankali ya furta"I will call
you". Murmushi kawai ta mishi tare da sunne kai.
By
Feenat Ja'afar.
[4/19, 9:28 AM] Feenat Ja'afar 馃鉁嶐煆� :
"JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
14_Washegari gidan Adama ta fara zuwa, ba
wata k'walliya tai ba,kawai "powder" ne da
janbaki sai "mascara".
Sanye take da "pink'' na doguwar riga kirar
'"Dubai'' wanda Ya Suleiman ya sai musu kan biki,
farin fashmina da ratsin pink ta faka gashin nan
kan ta nad'e shi cikin g'yalen, ta hau "hill",
matuka zaka zata y'ar wani mai kud'in ce,amma
tsabar rufin asirin Allah ne da had'uwa da iyaye
masu zuciyar yi.
Harara ta kai mata, "ai nayi fushi K'awa,
murmushi tai,a kiyi hakuri. Kai ta k'ada, "ya zanyi
toh? Ina su Umma? Murmushi tai, kan tace" suna
gaida amarya,jiya kad'ai har kin kara "shining "
dariya tai kan tace"dan ma yayanki ne.
Sai Bayan la'asar da k'yar Adama ta tabarta,dan
sau biyu mutumin ta na tambayar ko taje?.
A parlour ta same ta ita kad'ai, sai ta kara bin
parlourn da k'allo, tabbas iyaye sunyi rawar
gani,dan tsaf an fito da Aisha musamman
parlourn.
"Kai Allah sakawa iyayen mu da alkairi, Aisha
tace "Amin kam, sam ban tunanin zan samu rabin
kayan nan ba,Abba ga harkar gini shima yaya ga
auren shi,Furera k'warai Abba abin alfarin mu ne
wallahi... Kawai sai ta fara hawaye, tasowa tai
ta dawo kusan ta, kan ta goge mata ido, "Adu'a
zamu musu Allah ya kara musu bud'i,muma Allah
sa su more mu haka.
Kai ta k'ada tare fad'in "Amin. Nan ta hau kuma
fad'in kamar ta koma gida take ji,gaba d'aya tai
missing nasu.
" Ga nan ce fane muje man ki d'an d'aura min
daga inda kika t'saya y'ar K'anwata,,dan harara
ta sau mata,kan tace"kima zage,dan ba zuwa zan
nayi ba.
Sai k'arfe biyar suka shigo lokacin suna
kitchen,"Chief" tuni ta bud'ade gidan da kamshin
girki,"kai Furera mijin ki zai k'washi gara fa,
dariya tai kamin ta fara bawa Aisha shawarar
itama ko"Grace so amazing catering creations"
ta jona tunda "3month" ne. Tace zata tuntu6e
shi kuwa,bari a d'an k'wana biyu.
Da sallama suka shigo, sai d'ai ilahirin parlourn
ya d'ebi kamshin abincin amare. Zama yai yayin
da Ilyass yai hanyar "kitchen" yana zuba santin
kamshi cikin zolaya.
Shi kam gogan ido ya lumshe, sosai yana son
macen da ta iya girki,yasan tunda Aisha ta iya
toh prettyn shi ma ta iya.
Ita kam ganin ana neman mata fitsara a gabanta
yasa ta wanke hannu ta basu gu,a bak'in
"kitchen" d'in ta makale,tare da k'allon mutumin
ta yadda yake lumlumshe ido. Tsiyar Ilyass da
yake wa Furen ne ya sa shi bud'e ido,sai warai a
kanta,a hankali ya dago kai tare da zama d'ai-
d'ai, kanta kasa tana musu murmushin kunya.
Tabbas ance Wai ''in ka da k'yau, toh ka kara da
wanka" toh shi kam pretty da tayi wankan ko
batai ba tana burge shi matuka.
Sosai yake son karamin k'yau irin na "Prettyn"
shi,gashi ta iya dauk'ar wanka.
Murmushi yai tare da k'ada kai, Ilyass bai bar
kowa ba ashe? Hannunta Aisha ta rike tana
fad'in "rabu dashi sis,kan suka zauna a kan
kujera. Har suka gaisa da Aisha idon shi na
kanta.
Ilyass yace" madam, tashi mu basu gu su
sarara,dariya tai kan ta k'ada mishi kai sukai
d'aki.
Tasowa yai ya dawo kusa da ita ya tsugune tare
da d'aura yat'sanshi a kan le6en shi,ido kawai ya
zuba mata,kamar wanda yaga sabuwar halitta.
A hankali ta dago,tare da K'allonshi ido ciki-
ciki,sai tai murmushi tare da kara kasa da kai.
A k'alla ya kai kusan minti''5" kan tai
magana,"ina yini Uncle... Sai yai shiru bai amsa
ba, sai ta kara dagowa, kai ya k'ada mata,"Ba
Uncle daga yau Furii,ki bar wannan a makaranta,
K'allonshi tai, sai ya kara k'ada mata kai, "g'wara
ki ce ma AAA, "I like it,, murmushi tai, kan ta
k'ada kai.
Zama yai akan "center carpet" d'in, tare da
t'ang'washe kafarshi, kamar mai d'aukar
karatu,shi kanshi yakan rasa ya ake yake rasa
nutsuwar shi gun Furiin shi.
''Shin kina jin abinda nake ji a game da ke
pretty? Kai ta dago,kan ta zuba mishi ido,halamar
bata gane ba.
Murmushi yai,kan ya sada kai kasa,yana mai
fatan ta yarda dashi,d'uk da yasan mai wuya ne
ma taki yarda d'in.
"Pretty".. Ban san so ba sai a gare ki na samo,
tun wani lokaci achan baya zamanin "school"
nake jin irin " feeling " d'in nan, sai d'ai ban gane
meye shi ba.. Kai ya dago, idon ta a kanshi,ba ko
kiftawa, sai yai murmushi, "kar kiyi mamaki
Furera Muh'd,
Sai ya k'ada kai,kan ya tsare ta da ido,"I love you
more than you will ever know.. And I can't never
ever let you go again..
Ido ta rintse,tare da jin zuciyarta na tsanannta
bugu, kan ta farga ta kara jin wani sautin wanda
jinshi take tamkar waka yake raira mata dan
sanyin muryar shi... Da sauri tai kasa da kanta
kan tai ko'k'arin mai da kukanta.
Ya Ilahii.. Da gaske ne abinda take ji kuwa?
" ko d'ai yai batan kai ne? Kai anya? Toh ko
wannan shine batun da yace zai zo mata dashi?
A hankali ta sauke k'allonta a kanshi da shima
yake k'allonta dan jin tai shiru,zuciyarshi ce ke
faman buga mishi, tsoron shi d'aya kar dai Fure
tace bata son shi.
By
Feenat Ja'afar.
[4/19, 10:58 AM] Feenat Ja'afar 馃鉁嶐煆� :
"JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
15_"Ya ki kai shiru? Hope... Kai ta k'ada mishi,
"zan yi shawara.
Murmushi yai, " toh a son nawa za kiyi shawarar
ko a aure na? Murmushi tai kan tace"d'uk
Uncle..sorry.
Kai ya k'ada, "zaki ji ni gobe toh,amini kara d'ai.
Murmushi tai ganin ya ka'rkata kai.
Firar su suka ci gaba da yi ya koma kujerar kusa
da ita.
Waya ya zaro,kan ya bud'e" gallery" "you gotta
see this amazing
pictures.. K'ar6a tai a kunya ce, ganin ta a ciki
yai bala'in bata mamaki. Tana ina mey akai
wannan photonan masu yawa?
K'allonshi tai da halamar mamaki, gira ya daga
mata tare da kafada,sai ta marairaice mishi.
Sosai yake t'suma ta soyayyar shi,an ja aji kan ta
k'arbi tayin ta, sosai ta kara burge shi, dan bai
son budurwa mara kamun kai da aji, sai ya kara
bata wani girma na daban.
Gidan su yake mak'e kunya yaje,Amal kam kusan
kullum ranarta ce," ice cream " cheese " komai
ita,shi yasa sosai suka saba.
Ko kad'an bai nuna mata shi masu dashi
bane,asalima kusan kullum da mota d'aya yake
zuwa mata,sam bai kaunar rayuwar fa-fa.
Ba'a jima ba ya nemo k'anin Baban su da yayun
Mama suka zo tambaya, sai da ya tace su kan
yace su zasu,dan sarai yasan sauran yanzu sa
raina mishi tushen su Furen shi,d'uk da d'an
uwan Abban sai da ya tofa, sai d'ai ganin
dattakon Abban su Suleiman d'in yasa ya gane
d'an nasu gidan k'warai yabi ba wai dukiya ba.
Ginin su Abba da ya Suleiman yake musu yai
nisa sosai,har nashi a jiki yasa fili shima ya
had'a, dan haya shima ya kama.
Abba gidan shi na Zaria ya siyar wa yayan shi,
tuni ya chake mishi kud'i hannu ya bashi,har da
karin na bulo, d'uk da shi yana arzikin da zai iya
rike iyalin gidan k'anin nashi amma yakanyi
mamakin jajir cewa irin tashi,sam yafi son komai
yai da gumin shi da k'arfinshi.
Ahmad har gun aikin Abba yake zuwa in ya tashi
a shago suyi ta fira,tuni sai ya k'wanta mishi a
rai, dan ko motar da yake zuwa mishi da ita ka
gani kasan d'an masu hali ne,sai d'ai bai da
girman kai. Har aikin yakan ce zai taya Abba. Sai
kawai yai mishi dariya,dan sosai dan gayu ne,ina
shi ina aikin bak'in mai?.
Umma take tambaya kan wai Ahmad yace gobe
zasu gidan su gaida su Mama,tace ta bari Abban
su ya dawo tukun,. Ko da Abban ya dawo Umma
ta sanar shi yace ai ba damuwa,sai a had'ata da
wani rakiya.
A gado take suna waya kamar kullum, a hankali
maganar ke fita wanda na d'aki ma sai ya kula
kan yasan tana waya, idonta lumshe tana
saurararon yadda AAAn ta yake zuba mata
kalami masu sanyaya rai, tabbas yaci sunan shi
da ta kira shi da"SAHIBUL KALAM". Takanji wani
irin wutar sonshi na kara ruruwa cikin ranta,tun
tana kunya har ta ware tana aika mishi da nata
salon son.
Tunda ta sanar shi ya fesa wa Mama cikin
murna, tare da cewa Momy wai gobe zatai
bakuwa.
Sam bata kawo kom ba,sai tace mishi Allah ya
kaimu,har abin dad'i tasa tai mishi,"Momy pls da
hannun ki nake so,kai ta g'yada.. "Wannan k'wa
wacece haka? Hala y'ar makarantar ku ce?
Murmushi yai yace"eh kawai,dan yasan gobe da
budiri a gidan nan.
Washegari tana a gaban Amal tana g'yara mata
g'yaran gashin ta,ta zira mata "gown" "cotton
mai adon ja da yelo da ratsin fari,yana daga
kayan da tai fitar biki. Tai k'yau sosai,
tasa mata dan karamin hijab na yara fari da
takalinta choge fari,ba laifi,ko a y'ar masu kud'i
Amal ta fito,turare ta mika hannu ta bata wai ta
fesa mata na "Lailatul sahrA", kan itama ta hau
make-up, sosai tai k'yali iya k'yali, ga tasha
filawar baki da jan Rani.
Ak'wati ta bud'e tana neman kayan sawa, ta
fidda wannan ta kara ta ajiye,idonta kan material
ya kai wanda tama manta shi bata sa ba na fitar
biki,guda uku yayan su ya siya musu da amaryar
shi wai an kai office d'in su, dan " India " ne
"Orange", da filawa mai hoton ganye green an
gewaye shi da k'yallin"silver", murmushi tai dan
ganin" favorite " na Ahmad "Orange" musamman
a jikin mace. Zira su tai kan ta tsaya gaban
mirror ganin yadda d'inkin ya zauna mata cif!
Tuni ta hau d'auri, kai kace wata liyafar zata.
Tana cikin d'aura "buckle" d'in takalmin ta
"silver"data sa ranar "dinner" ta tsinkayi muryar
shi Umma na ya shigo. Da gudu Amal tai waje.
Tashi tai ta d'au g'yalen kayan da "poss" d'inta
ta yafa,gashin nan yai tum-tum a keya. Sai taja
g'yalen sama dan rufe gashin.
Tasan ko ina zata shiga a kasar nan, dan d'ai-
d'ai ruwa,d'ai-da'i t'saki.
Umma ce ta leko,"gashi fa,kai ta k'ada, sai
Umman ta karasa ciki d'uk.
Lalle tana yabawa da ya'yanta,sosai kamar sunyi
makarantar koyan k'walliya.
"Kinyi k'yau kam,sai d'ai naso hijab,amma ba
komai tunda an rufe kan, "ki gaida su sosai.
Kai ta g'yada, kan ta fita,a zaure ta sameshi shi
da mutuniyar,uwar magana,shi ko gajiya baya yi
da surutun Amal.
Sai d'ai suna ar'ba da ainashin madam d'in ya
kame,d'aidan wani, wai ka'rkataccen wani, a fili
ya furta "MashaAllah... Kai tai kasa dashi tana
murmushi, bata nufa ba taji "flashes" a hankali ta
dago,sai ya kara mata wani, kan ya d'auke
wayan ya k'alleta, sai yasa a ajihu,ya rike
hannun Amal suka jera, kamar wasu sabbin aure.
By
Feenat Ja'afar.
庐 NWA
9/29/16, 2:23 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 16_Shi ya bud'e mata,
cike da y'ar kunya ta shiga,ya bud'ewa Amal
baya. Cikin nut'suwa yake tuk'in, tamkar wanda
baison su isa inda zasu da wuri, firar Amal kawai
ke tashi, su kam murmushi kawai suke aika ma
juna,yau kam, tamkar siriki haka shima take d'an
kunyar shi, shi kam ganinta kawai yau na kara
mishi farin ciki. "Prettyn Uncle.. Da mamaki ta ju
ya,kan ta k'allo AAAn,sai ya daga mata gira, kai
ta d'an girgiza tare murmushi, kan ta dan harari
Amal wacce ke mata dariya," wa ya fad'a miki?
Da hannu ta nuna Ahmad, wanda ke musu
dariya,sai ta ju ya tare da d'aura kanta a kujerar
tana K'allonshi cikin wata siga. Yana "driving"
d'in ya ju yo kad'an, sai ya ga ta zuba mishi ido
tana d'an murmushi. Sai ya daga idon shi
halamun "ya akai? Kai ta d'an k'ada mishi tare
da sauke ajiyar zuciya. Sai ta koma kan titi tana
k'allo,wani irin farin ciki ta ji yana rat'sata. K'allo
shi tai lokacin da ta ga ya tsaya a gaban wani
waje kamar ''company" kato, sai yai murmushi,
kan yace "mun zo,yau za kiga Mama da Momy
da sauran k'anne na. Yake tai mishi, kan ta kara
k'allon yanayin gidan tun kan ma a shiga," Ya
ilahi!! Ina take shirin shiga? Mey ya sa Ahmad
bai nuna mata shi d'in d'an masu dashi ba ne har
haka?. " Gate" ne guda biyu a gidan,tafkeke ne
sosai, dan zai kai g'wan-g'wani d'aya, ita kam ba
mai shige-shige bace,sai d'ai gidan su k'awaye
masu d'an hannu da shuni,karara k'auyencin ta
ya so ya fito fili,bata tunanin ta ta6a shiga irin
wannan gidan a rayuwar ta. "Horn" yai,sai taji an
zuge ta ciki. "Subhanallah" shine kalmar da ta
ambata a bak'inta,lalle duniya na inda take.
"Flowers" d'in gidan su suka fara mata"welcome"
wanda suke a t'sare an musu "decoration " masu
ban sha'awa, d'uk gidan shimfid'e yake da
"interlock" tsari hudu ne a gidan,wato "parts" tsaf
sai ta karaya,da sauri tai kasa da kai gabanta na
fad'uwa. Ba d'ai Uncle Ahmad d'an gidan "Alhaji
Abba Ahmad" bane dan k'wangila? Sosai tana
yawan jin sakon gaisuwar shi musamman a radio
in Umman su ta kama, sannan ana yawan fira
dashi in harkar k'wangilar da aka bashi ta
kammalu musamman ta jaha. Kai ta dago,d'ai
d'ai yana "parking" kusa da wasu "arnun" ubansu
motoci,hankalinshi k'wance, sai ma murmushi da
yake ma Amal da take tambayar shi nan ne
gidan sun? Ummi yai ma waya,kan gasu kofa,
k'allota yai lokacin da ya gama wayar,"muje koh?
Kai ta k'ada mishi, sai ya fito ya bud'ewa
Amal,kan ya karaso ta ma bud'e, sai ya karasa
bud'e mata, d'an murmushi tai a takaice sai ga
nan Ummi ta fito. "Sannun ku Bros, da fara'ar ta
tai gun su, fara ce,kana ganinta ka ga Ahmad,
har fara'ar su d'aya. Itama da fara'a ta k'alleta,
sai ta k'alli Amal da tai wajen ta,dan fa d'uk
surutun ta toh a bakon waje miskila ce, ummin
ta d'an riko hannun Amal d'in sai ta make
kafada,sai ta mata murmushi tare da shafo
fuskarta da fad'in "fine girl". Murmushi yai,shi
yasa yake son Ummi a d'uk k'annen shi, ita
kad'ai ya yaba da nutsuwar ta,sannan yasan ba
zata bashi kunya ba. Bangaren Momy suka fara
shiga,kawai sai taji gabanta na fad'uwa tun da
suka doshi ciki. Kana gani kasan gidan y'an boko
ne,ko ina cikin tsari da k'yau, sosai yai k'yau,
kasan naira ta daku. Rukayya kawai ke parlourn
tana "chat" a "Facebook" shine a gaba,da
sallama ya shigo, a chan ciki ta amsa,dan jiya
tasu ta had'a su. Bai bi ta kanta ba yai d'akin
Momy. A y'atsine ta k'alli su Ummi,daga sama
har kasa ta ke k'allon Fure wacce Ummi take ce
mata ta zauna. Sam a d'uk y'an gidan basa shiri
da Ummi,dan ko k'allo suke ita ke damun su da
su tashi suyi sallah,gata sam bata raga mata,shi
yasa basa shiri,kai ta d'auke, da har zata tambayi
Ummin wacece ita??? Da fara'a Momyn ta fito
tare da shi, kai Furen ta duk'ar kasa,ita kam
Momy har ta zauna tana neman inda ta ta6a
ganin Fure. Sai ta amsa tare da k'allon Ahmad,
"daga ina bakuwar taka tazo? Dan sam ita bata
ga halamun wata hamshakiyar bakuwar da har ta
shiga kitchen dominta ba, duka-duka kayanta
basu wuce dubu 7 ba har g'yalen. Kai ya fara
sosawa yana d'an k'allon Ummi, sai tai
murmushi,kawai ba rufi tace" Momy budurwar
bros ce fa.... Wayar hannun Rukayya ce ta fad'i
kan tiles,wanda yasa d'uk suka zuba mata
ido,banda Momy dake k'allon Fure,a dirare tai
mata k'allon wulakanci,"ban gane budurwa ba
AAA?? A d'an takaice Fure ta juyo,dan tambayar
ta bata mamaki,sai d'ai mey,tabbas ta gane
matar nan,ita ce wacce Ahmad ya d'akko ta har
suka kusa maketa. Tabbas tai matukar tsorata
da yanayin Momyn,toh amma ya akai ta manta
da Momy uwar Ahmad ce har tazo gare su? Ido
ta rufe,dan kam bata ga halamun sassauci a gun
Momy ba tun wanchan karan bare yau. Dagowa
tai a hankali ta k'alli Ahmad d'in, dai-dai yana
rokon Momy da hannu kan tai hakuri kar ta bashi
kunya. Baki ta ta6e,kan ta tashi tai d'akinta. Sai
Rukayya ma ta tashi ta bita,tare da d'allawa Fure
harara, koh ta kan wayarta da ta fad'i bata bi ba.
Sanin hali, yasa Ummi tai saurin kat'se Fure da
cewa"muje bangaren Mama Auntyn mu,
murmushi ta k'ak'alo, wanda kana gani kaga na
dole. Sai ta k'allo Ahmad,kamar tace bazata
ba,dan a gun mahaifiyar shi ma bata samu
k'ar6uwa ba bare kishiyar ta? Sai d'ai yadda ya
marairaice mata yasa ta tashi,sai ya ruko hannun
Amal. By Feenat Ja'afar.
Like 路 2 路 Reply 路 Report 路 Apr 20
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 17_Kuka Rukayya ke
ma Momy,ita kuma na aikn lallashi,"ki ma bar
6ata hawayen ki akan wannan mummunar, zai zo
ya same ni ne, wato dan t'sabar yaso ci min
fuska shine harda sani na zage a "kitchen" wajen
girkawa wata shegiyar da koh a y'ar aiki bazan
d'auke ta ba.. "Momy ki ganta fa,daga gani sam
bata ma kama kafar dacewa dashi ba, amma ni ki
dubi irin yadda ake kaiwa rana akan yaja soni
yaki. Sai ta kara fashewa da kuka, tuni ta kara
tunzuro Momy, "ai ni na miki alkawarin zama
Matar Ahmad bah? Kai ta k'ada. "Toh kiyi kamar
ma baki ga ba. A parlour suka tarar da
Maman,rike da waya a hannunta, cikin nutsuwa
da fara'a take k'allonsu tana cigaba da wayar,ita
d'ai Fure a dirare ta zauna a bak'in kujerar,dan
sam bata ma k'alli Maman ba. "A,sannun ku da
zuwa, a d'an hankali ta dago ta k'alli
Momyn,Ahmad na zaune kusan ta,kamar zai
shige mata,kamarsu har ta 6aci da Maman sama
da Ummi,da sauri ta sunkuyar da kai tana
murmushi, kan a hankali tace"yauwa, sai ta zamo
daga kujerar ta gaida ta. Ganin haka Amal dake
kusan Ahmad ma ta gaida Maman. Da mamakin
ta sai taji ta amsa cikin mutunci harda tambayar
y'an gidan su. Amal Mama ta ruko," ya sunan
y'an matan, da fara'a Ahmad yace"Amal mama,
sai tai murmushi, "Aiya,ina ta samun labarin
Pretty, yau gani ga ita. Kai ta kara kasa dashi
cikin kunya. Lalle abin da mamaki,anya ba mama
bace Maman Ahmad?.. Maganar ta ne ta kat'se
tunanin Fure, "ki saki jikin ki fa, d'an kinzo gida
ne, ita d'ai murmushi kawai take. Ummi tace ta
kawo musu abin sha. Sosai mama ta ba ma Fure
mamaki,dan mace ce wayeyya,ga saukin kai,
sannan fara'arta ita tafi komai sa Fure nutsuwa.
Dan har ta shiga ciki ita da Amal da ta yarda
fuskarta sake,ta yiyu anan Ahmad da Ummi suka
gadi sakin fuska. "Auntyn mu kisha fa, ga nan
lodin abinci na jiran ku. Murmushi tai mata,bari
naje na dawo,kila bros ni ma tana kunya ta ne.
K'allon Furen yake da murmushi, sosai Ummi da
mama sun wanke shi gun Fure. Tana fita ya
dawo kusan ta ya zauna,tare da miko mata
lemon, k'ar6a tai tana k'allon shi,fuskarta da abu
biyu zuwa uku. Na farko mamaki,na biyu
murmushi, na uku tsoro. A rayuwa taki jinin
wulakanci, ta kuma tsani t'saki. Gashi d'uk ta
gani a bangaren Momy. Sosai sun mata
karamci,har bata ma san ta saki jiki dasu
ba,musamman Ummi. Da zasu tafi mama ta
cikata da sha tara ta arziki,har kofa ta rako
ta,sai d'ai da yace suyi ma Momy sallama sai da
taji dan dar! Suna zaune a parlour ita da Rukayya
sun cika sun bat'se, sai harara Rukayya ke aika
ma Fure,koh da yace zasu tafi, a wulance ba tare
da ta k'allo Furen ba tace"ta gaida gida. Abinci
ma bata samu ba bare sinkin mai. A mota tai
kok'arin d'annne ranta, ko'k'arin shi kar ta sa
abin Momy da Rukayya a rai,shi yasa yake ta
d'auke hankalinta da fira. Har gida suka shiga
dashi,yana rike da t'sarabar mama. Har suka rabu
bai ko mata maganar su Momy ba, amma Allah-
Allah yaje gida ya jima Ruky. Amal ke bawa
Umma labarin gidan da abinda suka ci,har sai da
g'wa6e mata baki, dan sosai Umma bata son
yawan magana. Sai dai ita Fure d'uk jikinta yai
sanyi tunda suka dawo. Ido kawai Umman ta
zuba mata. Su Hassan ne suka bud'e kayan suna
shigo wa,baki sake Umma ke bin kayan da k'allo,
A hankali ta fara daga su, Atamfofi biyu ne da
less, d'uk da batasan kud'in su ba amma taga
ana daga irinta a na kayan Aisha, tasan masu
uban t'sada ne. Ga wani uban Le's wanda zai kai
ashirin zuwa 30,ga "cosmetics " har da kud'in da
mama ta bawa Amal. D'uk sai jikin su yai
sanyi,Umma ta k'alli Fure,Furen ta k'alli
Umma,kowa ya kasa cewa komai. By Feenat
Ja'afar. 庐NWA Feenat.mywapblog.com
9/29/16, 2:24 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 18_Suna nan har Abba
ya shigo ta tashi ta tafi d'aki, a dirare ta k'wanta,
anya zata tila kanta a irin wannan gidan kuwa?
Sam bata ga halamun samun k'wanciyar hankali
a gidan ba sai gun mama,toh ya sauran y'an
uwan nashi zasu t'ar6e ta? Tana tsoron
wukanci,musamman a gun mai kud'i. Anya zata
auri A A Ahmad?... Tuni wata zuciyar tace "Ya
ya zakiyi da kaunar shi fa? Shi kike so ba wani
abinshi ba, sannan dashi zaki zauna. Da wannan
tunanin yau tai bacci. Washegari sukuku ta
tashi,d'an ma wai bata fad'a wa Umma mey akai
ba. Ya Suleiman Umma ke nuna wa kaya wanda
ya shigo gaida su, d'uk yaga jikinta yai sanyi, sai
yake tambayar ba'asi tace ita wulakancin masu
kud'i take gudarma y'arta. Sannan tana gudun
bak'in jama'a. Baki yai ta bama Umman,kan ba
komai sai alkairi. Da mamakin ta da Abba yaga
kaya sai bai ce komai ba sai fatan alkairi, hakan
yasa itama Umman jan bak'inta tai shiru. Sosai
take jin fad'uwar gaba in ta tuno su Momy, Anya
kuwa? Sai d'ai so da kaunar AAA takan mantar
ta d'uk wani abu da zai je ya kawo. Shikam yana
komawa d'akinshi ya shige,dan yasan sarai
idonshi yau,idon Momy. Sai d'ai ita da taji shiru
da kanta tazo jin ba'asi. Dowawar shi daga
masallacin isha'i kenan ya k'wanta tare da bud'e
hoton Fure na dazun yana k'allo. Kofa ya ji an
turo, ba ko sallama, sai ya dago,dan dabi'ar y'an
gidan ce haka yasan,irin dabi'ar da ya t'sana, sai
d'ai da mamakinshi yaga Momy,tashi yai tare da
k'akalo mata murmushi, harara ta aika mishi kan
ta nemi waje ta zauna. "Wato dan ka'rma nai
magana shine ko abinci baka je ci ba? Toh ni na
zo, sanin k'anka zancen Rukayya ne a gidan nan,
ba wai na wata chan ba,amma abin
mamaki,yanzu Abban ku wai yasan da
zance,kenan har ina gidan nan aje maka tambaya
ban sani ba koh? Kasa yai da kai, hakuri kawai
yake bata, dan yasan Momy, in ta huce ya
lalla6a kayarshi. "Ba ma wannan ba, tukun ka
kula da k'yau kamin ka so yarinyar nan har kake
neman shigo mana da ita gida? K'allonta yake,
sai ya girgiza kai, "na sani ai.. "Momy ina sane
fa,Furera mun juma, ni ne kawai ban fad'a ba...
"Ka rufe min baki, in haka ne Rukayya ma kun
juma ai,kuma ni ita na sani. Kai ya K'awar, kan
yace"amma Momy tun ba yau ba na sanar ki
Rukayya ba kala ta bace fa,dan Allah ki bar
zancen ta,taje itama ta samu miji, ni na samu
m... "Ahmad, cikin t'sawa Momyn ta kat'se shi, "
ni zaka ciwa fuska? Kai yai kasa dashi, yau
zazzagar arziki ta mishi,harda dan ba ita ta haifo
shi ba.. sai ta tashi tai waje,yana ta kiranta ta
doko kofa. Kai ya girgiza, a gaskiya bai son
fushin Momy,amma akan Rukayya zai yi komai
dan ganin ba'a manna mishi ita ba. K'wanciyar
shi yai, yana mai tunanin iko irin na Momy,
tabbas lokaci yayi da zaiyi "breaking" wannan
t'sarin na shigo da y'ar talaka zuri'ar su, shi
Pretty yake so, kuma ita zata zame mishi mata
da ikon Allah, fatan shi Allah ya taya shi yakin
nan,dan maganar Momy da ita ake gudanar da
komai a gidan. Bangaren Mama yaje cin
abinci,tasan yau kam za ai haka, amma ita y'ar
k'allo ce a t'sakanin su. "Ya suka je gida? Baki
ya wage,tuni sai ya ji ya ware,"Mama lafiya. Sai
da ya gama ci kan ya k'allo Maman tashi, "Mama
ai d'ai tayi koh? Murmushi tai,tare da ajiye waya,
"tayi kam,sai d'ai ya zakai da Rukayya Ahmad?
Maman yake k'allo da nazari,chan yace "Mama
sam Rukayya bata min ba,Momy ce d'ai ta
dage... Sai jim, "amma Mama ki taimaken wajen
ka'rfafa Furera gun Abba,nasan Momy shi kad'ai
zai iya hanata yi min dole. Kai ta k'ada, sosai
take tausayin yaran ta,musamman yadda suka
k'waso dabi'ar Momy goyon Momy, guda d'aya
ya fita zakka ciki, akan Ahmad kam baza ta bari
Momy tai nasara ba InshaAllah, a wajenta da
talaka da mai kud'i d'uk d'aya ne. Sai d'ai tace
ya lalla6a Momyn. Sosai ya ji dad'i, shi yasa
yake kara kaunar Mama. Dan tana son abinda
yake so. Washegari kamar kullum yazo gaida ta
tai banza dashi tare da juyar da kai, sai yai
murmushi, kan yaje inda ta juya, tsugunawa yai
tare da dafa hannunshi a cinyarta, hakuri ya fara
bata,kan ba yadda ta d'auka yake nufi ba. Da
k'yar ya samu ta d'aina fushi,sai dai har yanzun
tana kan bakarta na Rukayya ta sani,k'yaleta yai
tare da lalla6a ta,dan a rabu lafiya. By Feenat
Ja'afar.
9/29/16, 2:27 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 19_Tun daga wannan
rana ya gama fito wa da Fure ainashin shi
waye,tarihin su,fa komai,har hamdala tai a
zuciyarta da taji ba Momy ce ta haifo shi
ba,hakan yasa ta ware suka cigaba da fahimtar
juna. Yanzu kam fachaka ya fara mata,sai d'ai
kullum in ya bata sai sunyi fad'a, wataran ma sai
d'ai ya kai wa Umma da kanshi. Sai dai sosai
yana jin dad'in yadda take nuna abin duniya bai
dameta ba. Chargy yasa a parlourn Momy yaje
masallacin azahar,Rukayya ce ta shigo parlourn
dan zaman charting. Sai ta kula da wayan
shi,kawai sai ta raya mata bincike cikinta.
Sunkuye take da kai tana murmushi ta d'an rike
g'yale,"eye lashes" nata sunyi zara-zara, hoton
ya manna a "screen" na wayar shi,
"Mtsww,banza kawai, sai ta k'ada kai, kawai sai
ta shiga cikin "gallery" ta hau "deleting" d'uk
wani hoton Fure da yai "editing" yasa "pretty".
Sai da ta goge d'uk "foldern'' kan ta shiga
"contact". Bataga wani sunan mata ba sai na
y'an gidan, ko numbern ta babu,sai ga "pretty"
ya fito, wayarta ta d'akko ta k'wafi numbern tana
surutu ita kad'ai, tana gama k'wafa tai "deleting",
ta ajiye wayar kamar ba'a ta6a tai ta zauna. Bai
shigo ba sai bayan la'asar, shima sai da ya
tabbatar ya gama shirin zuwa gun Fure yazo cire
chargy, "blank" ba komai kan screen d'in, sai yai
tunanin "memory" ne ya goce,yana k'allonta yai
kamar bai ganta ba,zama yai g'yara memory, ita
kam dariya take kunshe wa, yanayin shi d'uk ya
sauya,fuska had'e ya k'allo ta,da sauri ta gintse
dariyarta ta d'aina K'allonshi. A masife yai yo
kanta, "Kina hauka ne?...Yaushe na zama abin
wasan ki? Tashi tai tana k'unk'uni, "mey na ma
toh? Wayar ya k'alla,ji yake kamar ya rufe ta da
duka,ihun da yake wa Rukayya ne ya fito da
Momy, yana ganinta bai hana ya gama sauke
komai ba, "lafiya? Kai kawai ya gad'a yai
waje,yana fita ta hau dariya. Abinda y faru ta
fad'awa Momyn,tace ta mata d'ai-d'ai. A mota
t'saki kawai yake,Allah ya so shi ya tura su
"system" nashi, a hakan zai yarda da auran
Rukayya? Yarinya marar K'wak'walwa? Yai t'saki.
Da k'yar ya seta kanshi kan yaje gun Fure. Ita
kam Rukayya yana fita sai tai tunanin ba gun
Fure za shi ba, cewa Momy tai tana zuwa,
d'akinsu tai,ta k'wanta kan ta fara kiran layin
Fure. A zaure suke,kamar kullum suna tad'in su
cikin nishad'i,ga Amal a gefe tana mota. Wayan
Furen ne tai kara,sai ta k'allo shi da murmushi,
kai ya k'ada mata, dan ko shi aka kira in dai suna
tare sai ya nemi izinin Pretty kan ya daga.
Number ce, cikin nutsuwa tai sallama, sai d'ai ita
daga chan da zagi ta bud'e taron. Yadda fuskarta
ta sauya ne yasa yake k'allonta, sai ta k'ak'alo
murmushin dole tana cigaba da sauraran
Rukky,batasan speakern yana d'an ji kad'an ba.
"Kina magana da Rukayya matar Ahmad bada
jimawa ba.. "Y'ar matsiyata kawai, ai nasan
kinsan ba ajinki bane shi, ki fita gona ta,dan Ya
Ahmad nawa ne ni kad'ai... "Nice zabin y'an
gidan nan, so tun wuri kisan inda dare ya miki..
Tashi tai,da hannu take nuna mishi tana
zuwa,tana shiga d'aki tana jin yadda take aikawa
iyayenta zagi. Murmushi tai, kan tace "Furera
ikon Allah,toh a gaskiya bazan iya musayar yawu
da wacce bata isa inda take tunanin ta isan ba...
"AAA na Fure ne kad'ai, wallahi k'walelen
ki,tunda anyi k'wantai a fad'i haka man... " uban
wa yai k'wantai? T'saki Furen tai, kan tace"Allah
kat'se miki wahala, dan kin haukace... Kit ta
kashe wayarta. Kanta ta g'yara,kan tai zauren
d'auke da murmushi, kawai Rukayya y
bada,amma da mamakin shi sai tace wai "wrong
number" ne,shi d'ai yaji sunan Rukayya a
wayar,kawai sai ya share suka ci gaba da tad'in
su. "Sai rowar hoton nan ake min,yau d'ai a
d'akko min naga. Kai ta k'ada, kan ta tashi,
dama dan ya d'au number ne, cikin sauri yai
copying zuwa wayarshi yai dailing sai ya kashe
da sauri. Har ya tafi bata fad'a mishi komai ba.
Yana zuwa parlour ya zauna,lokacin Rukayyan
tasa chargy, dailing ya fara,sai yaji a rufe,kawai
sai yaje ya duba,a rufe take,dan ya tabbatar ya
k'unna, sai k'wa ga kira ya shiga. Da gudunta ta
fito,a zatan ta,murmushi kawai yayi,ya ajiye ya
wuce. Sai d'ai a ranshi ya sa zai bawa Rukayya
mamaki,dan ko zata mutu bazai aureta ba.
T'sawan kusan wata 7 yanzu kenan da had'uwar
su, biki saura wata d'aya dan tana exams, amma
naira biyar bata ta6a rokarshi ba, shi yasa yake
d'aukan Fure ta daban cikin mata. Hakan yasa
yau yace zai g'wada ta, suna a zaure suna tad'in
su cikin so ya k'allota. "Pretty, kai ta dago tare
da amsawa, sai ya k'alli Amal da ta zuba musu
ido,sai yai murmushi, " ga nan biki sai karato wa
yake amma baki nemi komai ba. Murmushi tai,
kan ta k'alli gefe, "Yanzun kam bana bukatar
komai gaskiya, in ma za'a bukata su Ummi zasu
ma magana. K'allonta yake, yasan in ya biye
mata da gasken bazata tambaya ba, "toh ke da
kanki ba ki bukatar komai? Nasan dasu Ummi, da
pretty nake. Murmushi tai, kan ta k'ada kai,
"eh,na sani. Kai ya k'ada, sai ya tashi yace ta
d'an jira shi, ya nufi mota. Da babbar leda ya
dawo,d'auke da k'wali a leda. Ita d'ai nata ido,
"karan nan pretty ban son musu, kai ta daga, sai
ya ajiye mata ledar kayan a gabanta kan ya
zauna da dayar. Zaro k'walin yai,sai ga nan waya
zankadediya ta fito, sai ya cire recit d'in kan ya
mika mata. Idon shi take k'allo, sai yasha
mur,dan yasan yanzu sai tai mai musu, k'ar6a tai
kan ta tsaya neman ba'asi. "Ta ki ce,en bana son
musu, wayar take juyawa,koh wata uku bai yi da
siya mata ta hannunta ba,sai d'ai ba bak'in
magana. Takalma ne kusan kala uku masu k'yau
dad'in zuwa "dinner". Sai kud'i aciki masu yawa,
text taji ya shigo wayan ta,wai ta amfani da
kud'in. Sai tai murmushi, ta kaima Umma su,dan
dama takalmi da sarka ne kawai bata siya ba.
Ginin su Abba fenti kawai ya rage, Umma tafi
kowa murnar su tare ko dan auren Fure. Ana
saura k'wana goma biki ya sanarta y'an gidan su
zasu suzo kawo kaya. Gidan Adama taje dan
Aisha tana fama da kanta suka musu pepee
chicken. By Feenat Ja'afar.
Like 路 Reply 路 Report 路 Apr 23
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 20_Ganin kayan auren
Ahmad ba karamin kuka Rukky tai ba, bori take
na gaske,wannan karan kam anfi k'arfin
Momy,dan Abba ya shiga zancen dumu dumu.
Hakuri kawai take bata,kan ko ba yanzu ba
kamar ta auri Ahmad an gama ne. Washegari
mota hudu sukai dan zuwa kai lefen Fure,daga
nan zasu kai na d'ayar amaryar k'anin Ahmad.
Tunda aka t'saya a kofar suke tantama, "anya
nan ne? Waya Aunty JIDDA ta d'auka, kan ta kira
Ahmad d'in, "ka yi k'watancen nan d'ai-d'ai
kuwa? Jim tai tana sauraran shi, kan ta k'alli
sauran y'an uwan nasu da y'an uwan iyayen su.
"wai fa nan ne,har nanata min yake wani gidan
kasa mai zaure.. Tai k'wafa,tunda naji artabun da
ake dashi nasan ba haka aka bar yaron nan
ba,yanzu ki duba wai gidan da zamu kai wannan
uban kayan? Wato shi yasa yake boye ta fir yaki
kawo ta mu gaisa. T'saki Huwaila (Sa'adatu)tai,
"Aunty shi fa ya jiwo, ku y'an aike ne, suma
sauran d'uk jikin su yai sanyi,banda y'an uwan
mama, wanda ta sanar su komai. Bai fi mutum
uku bane sukai sallama,kowa fuska d'aure,sosai
suka rainawa Ahmad, karewa gidan k'allo
suke,Fure dake d'aki tana leken su ta window,
daga mai ta6e baki,sai mai y'atsine fuska,kalilan
ne aciki wanda fuskarsu a sake, zama tai a kan
katifa, ganan abinda taki jini,raini,wato sun raina
mazaunin ta? Zaman kirki basuyi ba aka basu
tsarabar su da tukuici,y'an uwan mama ne suka
k'ar6a harda godiya,sukam tuni sunyi waje. Allah
ya so su makociya d'aya ce,sai y'an uwan su na
Zaria, dasu Adama da Aisha, kowa jikin shi yai
sanyi da dangin mijin da Fure zata aura,barin
Umma. Kaya ne gasu kamar ba gobe Ahmad
yasa aka tulo su,sai san barka. Da dare suna
zaune har da Furen ana nunawa Abba kaya, ita
d'ai Umma roko take ai ai fenti su tare ko a
daina ma y'arsu gani gani. A ganinta wai Tuwan
girma miyarshi nama. Murmushi Furen tai da
d'an guntun hawayenta, kan ta k'allo su Umma,
"Umma d'an guntun gatarinka wai yafi sari ka
bani, ni d'ai ina alfari da tushe na... Hawaye ta
goge, k'warai auran nan ya fice mata aka, ji take
tamkar tace ta fasa. ''Abba dan Allah ko an
gama komai kar ku tare sai bayan bikin nan,
Umma nan ne asalinmu, dan Allah a min wannan
alfarmar, mu zauna anan, ba ruwa na da zancen
su, tunda d'ai shi ya ji ya gani. Murmushi Abba
yai, shi yasa yake alfahari da Furen sa, d'uk D'a
na k'warai mai kishin tushen shi ne k'warai. Kai
ya jinjina, kan ya k'alli Umma da jikinta d'uk yai
sanyi. "Nima nayi tunanin nan,kiyi hakuri Umman
su,kiji kawai ki kiji, har a watse lafiya. Kai ta
jinjina, sai Furen ta basu waje,bata jima da shiga
ba sai ga kiran Ahmad d'in. Yadda take amsa
wayar yasan tabbas tana a damuwa, wanda
yasan bazai wuce na y'an gidan su ba. Dan
yanzun barin cikin gidan suna ta kace nace akan
gidan su Fure,su basu ga abin zagwadi a y'ar
gidan ba da har zai ki Rukky. "Kiyi hakuri pretty,
ni ne mai auren ki,InshaAllah zaki same ni mai
rike amanar ki cikin aminci. Da mamaki take
sauararen shi, da sannu sai da ya wanke laifin
y'an uwanshi cikin lumuna, har taji zata iya ji ta
gani wajen zama dasu. Haka k'wa akai,gini ya
kammalu amma Abba yace sai bayan biki, y'an
uwa wasu na neman ba'asi sai yace musu kawai
ba dalili. Fatan shi Allah yasa alkairi cikin auren
Furen shi,kodan mutuncin Ahmad a gun shi, ko
da Ya Suleiman yace ma Adama su su tare sai
tace mishi abari su tare dasu Umma. By Feenat
Ja'afar.
Like 路 Reply 路 Report 路 Apr 23
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 21_Gaban madubi take
a gidan Aisha,kowa yana yaba yadda tai k'yau.
Yake kawai take musu,sosai itama tasan tai
k'yau, "net" ne "brown" da ratsin "golden" na
doguwar riga yai mata cif-cif. An nada mata
g'warg'waro shima "golden", a d'aya a takalmin
Ahmad da ya bata kan biki ta d'au wani ubansu
"golden" ta sa,kai kace da "gold" akayi shi,rike
da "poss" irin takalmin. G'yaran jikin da ta samu
ne yasa fatarta kara gogewa ta dawo ruwan
itama "golden" d'in, sosai ta barar da k'yau a
wannan rana, idon nan kad'ai ke fari kamar tai
"fixing" na "lashes", ga yasha "Eye shadow" abin
ba'a cewa komai, a gaskiya in kaga Fure a ranar
bazaka d'auka ba bikin wata y'ar Attajirin
bace,komai ya ji,an t'sat'so k'yau sosai. D'uk
wani sukuku take jin ranta tunda aka d'aura
auren. "Dinner " za su, wayan ta ke kara
tsohuwarta ta da, sam a ganinta in ta rike
sabuwar kowa yasan daga gun shi ne, sai ta bari
sai ta shiga daga gidan shi ta fara amfani da ita.
Cikin sanyin murya tai mishi sallama. Sai ya
jingina a jikin kujera jin muryar har k'wanyar
kanshi,Ilyass dake tuki yai murmushi. Har cikin
gidan Ilyass ya shiga,kan amarya ta fito da
sauran k'awaye. Kanta kasa suka fito ita da
Aisha da Adama, da kanshi ya fito daga gaban
motar ya bud'e mata gidan baya. Shima sai ya
zaga d'aya bangaren, dariya suka hau mishi,sai
Ilyass yace Aishan ta shiga gaba suje Adama ta
jira mijinta, sauran suka shiga suma mota. Tafe
suke Ilyass na ta musu shakiyanci sukam sai
murmushi suke, a hankali ya k'allota,sai tai kasa
da kai tana murmushi. Yasha riga malum-malum
na farin shadda,an mishi aiki da zare brown, yai
k'yau sosai,hular shi ma "brown" sai kamshi yake
zubawa. Sosai yake k'allonta dan tun jiya rabon
da ya ganta har aka d'aura Aure, wanda ita har
kunya ya fara bata. Hannunta yake k'allo, wanda
suka sha "bangles" manya kamar na gold da
zobuna manya. Ga kunshin nan ya hau kasan su
sai suka mishi k'yau. Bata aune ba taji shi rike
da y'atsunta, tuni taji wani abu ya tsirga
mata,yayinda gogan ajiyar zuciya ya saka, yasan
ya kare iyakar Allah sosai,yau ne farin ta6a
hannun macen da ba muharama sa ba, gashi yau
ta zama mallakin shi halali. Shi ko wannan "pre-
weeding" pic d'in da ake d'auka a rungumi juna
sam bai mishi ba, dan a ganin shi duk abinda zai
kai ka ga sa6on Allah sam bai burge shi. Yadda
take lumshe ido d'ayan hannunta na kan bak'inta
sai ta kara kawatuwa mishi, dole yace"D'ukkan
godiya ta tabbata ga Ubangijin talikai, ya gode
Allah da yau Prettyn shi ta zama tashi a yau. Har
suka isa gun "dinner" yana rike da hannuntan.
Suna tsayawa akazo bud'e musu kofa, sai ya
daga musu hannu kan shi zai bud'e mata, hooo,
kowa ya birgisu, hannu ya mika mata wai ta rike
ta fito, ganin an d'aura yasa ba musu ta bashi,
sai d'ai fir yaki cika mata hannu,a haka suka jera
cikin "Hall" d'in kanta kasa d'auke da murmushi.
Tuni su d'ayan Angon sun hallara da amaryar shi
su kawai ake jira. "Flashes" ake basu ta ko'ina,
Fure fa ta bada kala,dan ko y'ar masu kud'in
bata fita da kom ba sai d'ai k'yau. Su kansu su
Aunty JIDDAN sai suka ga shigarta tafi k'yau,
amma haushinta ya hana su yaba. Barin Rukayya
ganin su rike da hannun juna kamar ta kurma ihu.
An fara program aka umarci ango da Amarya su
fito su yanka "cake". Hannunshi na kan nata
suka yanka, cikin jin kunya ta sa mishi a baki, da
wasa shima yake kokarin sa mata ya dan shafi "
lips " nata,kowa ya zuba musu ido,ba kunya ya
kai hannu zai goge mata sai ta dan k'alleshi, mai
hoto kuma ya d'auka a hakan. Sosai sunyi k'au,
Ahmad yana ta barin SO a hall, yayinda masu
t'saki nayi masu murmushi nayi,masu musu tafi
sunai,su Rukky kam baki ta ta6e. Rawa aka ai
bayan an cigaba da "program''. Kai ta girgiza
mishi, sai ta burge shi, ita kam d'ayar amaryar
sai taka rawa take ita a dole wayayya ba ko
kunya. Ana tashi ya k'arbi "key" wai shi zai kai
matar shi. Sukam su Ya Suleiman nasu dariya
ce. Ba musu ya mika mishi mukulli. A hankali
yake jan su a sabuwar motarshi da siya musu shi
da Prettyn shi, ita kam yau d'uk kunya yake bata.
Shi yasa kanta na k'allon glass d'in gefenta da
murmushi. Ba tasan irin farin cikin da yau take ji
ba. Ga wata kauna da taga Ahmad na nuna mata,
wanda a ganinta koh ita ta isa sata tai zaman
auren shi. Wakar shi ta kullum ya sauya, tuni ta
fara taken "Nothing gonna change my love for
you.. If I had to live my life without you near me
The days would all be empty The nights would
seem so long With you I see forever oh so clearly
I might have been in love before But it never felt
this strong Our dreams are young and we both
know They'll take us where we want to go Hold
me now Touch me now I don't want to live
without you. Jingina tai tare da lumshe ido cikin
murmushi, sosai baitin ke shigarta,sai ta tuno
wani lokaci achan baya,kawai bata nufa ba taji ta
dara,har hak'waranta suka baiyana, d'ai-d'ai taka
burkin da gogan yaci. Da sauri ta bud'e ido jin
sun tsaya,dan baici ace sunzo ba. Taga titin ba
abinda ya faru, sai ta juyo da k'allonta gare
shi,tagumi ya da hannu d'aya yake k'allonta, sai
ta daga mishi gira halamar lafiya?... Kar ya
fad'arsu yasa ya taka birki. Kai girgiza mata, tare
da sauke ajiyar zuciya. Shi kanshi bazaice ga
adadin son da yake ma Pretty ba,sannan wakar
nan tana kara rura wutar Sonta ne a kullum.
Matsowa yai da fuskar shi d'ai-d'ai tata har
numfashin su na had'uwa da na juna, sai taja
tata baya tare da K'awar da kai tana murmushin
kunya. Hannu yasa ya juyo da ita,sai tai kasa da
kai, a hankali ya rage "volume",tuni ya hau tsuma
zuciyarta da kalamai wanda bata ma san ta dago
tana k'allon shi ba. K'warai sakon aiken ido yafi
isa cikin sauri, hakan da tai sai ya bashi damar
aika sakon shi tanan. Gaba d'aya sai da ya gama
kashe mata jiki da tad'in shi,wanda ita bata san
ya iya irin shi ba,sosai yakance yana Sonta har
ba iyaka, amma kalaman yau na daban ne.
Karshe sai da ya sada ta da jikin shi ya samu
sa'ida,ita kam lum tai kamar ta samu pillown ta.
Chan kuma sai ta hau kiciniyar K'wacewa, d'uk
da glass d'in baki ne. Dagowa yai da lumsassun
ido yana duben ta," yanzu sai gobe za'a kai min
ke? Kai ta lang'wa6e mishi, cikin marairaita. Sai
ya zuba ma bak'inta ido wanda yasha janbaki mai
k'yau "brown'' mai shekin golden, ganin ya kawo
fuskarshi tata yasa ta saurin rufe ido. Sai ya
tsaya k'allonta da murmushi, ganin yadda ta wani
tamke ido,hannu ya kai kan idon sai ta bud'e a
hankali,bata aune ba taji sabon al'amari, ba shiri
ta kara rufe idon. Shikam kamshin strawberry ma
kamar yake ji a bak'in,ga dan zakin "lips" d'in
nata. Dan kanshi ya batta,kan ya hau cigaba da
kallonta, idon nan a rufe... "Horn" d'in su Ilyass
ne da har sun gama sa jama'a gashi har sun
cimmusu suna nan. Take sai tai gefe da kanta ta
boye cikin kunya,kai ya k'ada, kan yai murmushi
ya tada mota. Yasan yau sai d'ai ya toshe
k'unnenshi agun Ilyass,tunda har ya cimmasa. By
Feenat Ja'afar.
Like 路 Reply 路 Report 路 Apr 23
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 22_Har suka rabu taki
bari ya ga fuskar, Ashe AAA haka yake? Hmm ita
kuma ga kunya. Haka ya hakura sukai sallama
yana fad'in "I Love you... Jim tai,kan ta shiga
gida kamin ya k'ada kai shima ya wuce. Lekowa
tai daga zauren da ta la6e , sai ta koma ganin ya
wuce ta jingina da bango cikin murmushi ta dafe
kirji tana maida numfashi,tamkar wacce tai wani
tseren. A hankali ta kai hannunta kan "lips" nata
tana tuno dazun, "Love you too AAA,wai kuma
sai tasa tafin hannu ta rufe fuska ita a dole
kunya, sai ta k'ada kai tai cikin gida. Tuki yake
yana shafo "lips" nashi,harda dubawa a "mirror''
yana murmushi. A hankali ya sauke ajiyar zuciya,
" Furii" "Pretty"..sai ya sau murmushi, kan a
hankali ya furta "I Love you" kamar tana k'allon
shi. Biki anyi cikin aminci, sai d'ai har aka gama
ba wanda ya kara leko kafarshi gidan su Fure sai
y'an uwan mama da Abba, hatta d'aukar amarya
basu zo ba,sai suka tafi d'aukar d'ayar amaryar.
Haka Fure naji aka tafi da ita ta rabu dasu
Umman ta. Sai d'ai fatan Allah kad'ai hau. Y'an
mata aka kai,ba tare da tsayawa wani siyan baki
ba,a ganin sun wuce ajin inji Ilyass. Wasu suka
tsaya yiwa Ango da Amarya fad'a. Yana rakasu
ta koma d'aki. A gaskiya iyaye sun mata ba zata,
sam bazakai t'sammanin ba y'ar masu dashi
bace,d'uk kamar wanchan karan karan nan ma
kawunsu na Zaria ne ya mata gado da
kujeru,shikam da zamani yake tafiya, shi yasa
koman su tsaf-tsaf. K'wance take tana kara
duben yanayin d'akin,sai ajiyar zuciya take na
wacce taci kuka, sosai ya mata k'yau, ga wasu
arnun labulaye, Allah sarki Abban ta da Ya
Suleiman, Yanzu ta yarda da wadatar zuci tafi ta
kud'i. Fatan ta Allah ya kaita lokacin da zata
rama musu itama. A haka har ya cimmata a
d'akin. Tsayawa yai yana k'allon ta, sai ta tashi
ta takure kanta tare da jingina a jikin allon
gadon. Sallama yai,sai ta duk'ar da kai ta amsa,
zama yai kusa da ita yana k'allon yadda d'uk ta
bata k'walliya da kuka,, shi a kullum yana da
tambaya ga mata,wai shin mey ke sasu kuka in
za'a kawo su gidan aure? A ganin shi farin ciki
yafi kamata suyi su kuma gode wa Allah. Hmm..
Bazaka gane ba AAA. Ya ya iyah,aikin lallashi ya
hau yi, sai d'ai dama bai ba,dan kuwa ya
jang'wa6o ta. Kuma fa ta manne mishi,amma
tana fad'in su Umma...Lol. Kamar wata yarinya
ya hau hura mata k'unne. Tuni k'wa sai ta nemi
kuka ta rasa,ya tafi garin su. Da dabara yai ta
janta har ta ware tana murmushi k'eta. A haka
har suka gabatar da da sallah kan ya d'akko
komai a "parlour" da "plate'. Haka ba dan dad'i
sai dan ya mat'sa mata taci kad'an. Ta tashi ta
k'washe kayan,a kitchen ta t'saya k'allo, lalle
duniya,wani abin ma bata san dashi ba. Ga nan
"gas cooker" da halamun mai gidan yasa. Dan
harda gidan ta. Ya shiga d'aki ta dawo parlourn,
shima ba laifi an mata bajinta d'ai-d'ai k'arfi,
kujerunta masu "Ledar" ne kalar 'Orange' da
"milky" labulan ma haka, ga dan "center carpet"
nata mai "grass" da "table" mai zanen "heart" a
jiki. Sai TVn ta "plasma" manne, sun had'a mata
"home theatre" dai,ga nan wata "flower" a tsaye
kamar g'wada da da ya'yanta "Orange''. Ajiyar
zuciya tai,jin an bud'e kofa. A hankali ta zauna a
kasa,yayinda shi kuma yai wajen TV, ashe har
sun had'a. Kujerar da take ya dawo da "remote"
a hannunshi, sai ya tasa kanshi a cinyarta yana
k'allon fuskarta da murmushi. Itama murmushin
take,amma cike da kunya, sai ya juya kan TV ya
d'anna "play". "Title" taga na "My heart will go
on... Wani page ya fito da ire-iren pic din da yake
d'aukan ta ta daga kai sama tana dariya har
hak'waran ta sun fito, Sai ya rubuta. To my
darling Furii.... Sai ga nan wakar "Celine Dion" na
"every night in my dream tana yi cikin "slow
motion" ta fara. Wani pic d'in ya shigo shima tai
k'yau, a kasa yasa.. "I have been in love with you
from the very moment I met you and every day I
continue to fall deeper in love with you".....
K'allonshi tai, tama kasa magana,dan sam wasu
ma bata san an d'auka ba,sukanyi dai fira
wataran taga kamar yana d'aukar ta hoto. Har ya
kare yana mai fallasa mata sirrin ranshi ne kawai
a gare ta,sosai ta gamsu da ganin abin, ya
kayatar ta.. K'allonshi kawai take tana tunanin da
gaske tun had'uwar su ta farko ya fara Sonta?
Ganin k'allon ba na karau bane yasa ya dawo
fad'i da bak'in shi, ina Fure bazata iya d'auka ba,
dan bataji ko ita tana mishi irin wannan son da
yake ta k'wadata da shi. Kan su farga har dare
ya ja sosai,tasan in zasu k'wana haka yana fad'a
mata irin kalaman nan toh bazata gaji da
sauraron shi ba. Ahmad kam karshe ne, ya kere
ta a komai, sai d'ai ya zame mata dole tai
ko'k'arin finshi iya kalami, a ganinta ita ya dace
ta haddace. By Feenat Ja'afar. 庐NWA.
9/29/16, 2:28 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 23_K'allon yaje ya
kashe,dan jin TV na kukan a kashe ta ta kare,
sai ya ajiye "remote" d'in tare da juyo wa gare
ta, shi take k'allo, sai yai murmushi tare da zuwa
da t'sugunawa a gabanta kamar mai neman tuba.
Abin ba na magana bane a gare su, sai yasa
hannu ya ware g'yalen da ta nad'a, ya cire
d'ank'walin, sai ya ciro da ribbons d'in da ta
tufke kanta da ya sha "relaxer'' d'ai-d'ai fankar
"parlourn" ta k'ada gare su,tuni sai gashin ya
fara tashi, ina gogan baki ya saka,ganin yalasha,
tare da fad'in "SUBHANALLAH.... Hannu tasa ta
rufe fuska,dan sai ya bata kunya ma, cikin ranshi
kuwa,fad'i yake "Lalle t'sarki ya tabbata ga
Ubangijin Sammai.. Ubangijin d'aya k'era mishi
FURIIN shi mai saukin k'yau a baiyane, sannan
mai t'sananin k'yau a ciki.. Ashe Allah idan ya
hana k'yaun fuska,sai kaga ya baka k'yaun jiki...
Yanzu ya yarda kowacce mace mai k'yau ce, ina
ma Y'an uwan shi zasu d'aina zaban k'yalk'yal
banza, suje su lalumo irin wanda basa so da yai
imani su da auren mai k'yau sai d'ai-d'ai... Shidai
yace "ALHAMDULILLAH.. Ganin irin "postern'' da
yai yasa ta zamu itama tai yadda yai, sannan ta
hau fad'in cewar ita ce fa,ba wai sabuwa ba. Sai
yai murmushi kan ya tashi t'saye,sai ta bishi da
k'allo, hannunta ya riko tare da tasarta t'saye
suna fuskantar juna. Jin ba zaya jure ba yasa
bata nufa ba taji ta asama ya d'auke ta kamar
wata baby, sai ta sunne kai kamar marar lafiyar
da aka d'akko ta kasa tafiya. Gun fanka suka
je,sai ta mika hannu ta kashe, tare da sak'alo
wuyan shi. A gado ya zaunarta, sai shima ya
zauna tare da shafo kanta, halamun d'ai gashin
ya mishi, sai tai murmushi tare da sadda kai
kasa tana wasa da awarwaron ta. Sai shima ya
kama hannun, a hankali ya kai shi d'ai-d'ai fuska
yana k'allon filawar da ta fito da taimakon
hasken "bed lamp",cikin nutsuwa ya fara zame
su a hankali, babu magana sai d'ai murmushi.
Sannu a hankali har d'an k'unne ya tayata cire
wa,,kan ya cigaba da rera mata wakar dake
mantar ta kanta ma, sosai in da so,toh komai ya
kan tafi a sauki, sai d'ai fa Furii rakin nan daga
baya yasha shi, tushe k'unne kawai yai, kan daga
baya ya ji da lallashin. Asuba nayi ta bud'e ido,
yana rike da hannunta ya durkusa gabanta,kamar
mai neman ta inda zai fara tada yake, murmushi
ya sau mata,tare da kai hannu ya g'yara mata
gashin ta,sai ta k'au da fuska itama da
murmushin,sai dai hawaye na k'waranya. Ganin
har za'a tada sallah yaki tafiya yasa ta yunkura
zata mike, sai ya taso dan taimako, kai ta
girgiza, kan tace zata iya. Da k'yar ta lalla6a ya
tafi,kan tai dabarar tashi. Yau d'uk sujjada sai
Furii ta samu adu'a, har bazai ce ga adadi
ba,fatan shi Allah ya basu zuri'a da Fure daiyiba
masu t'sant'sar tarbiya irinta. Kan ya dawo ta
kimt'sa komai har ta kara k'wanciya. Haka ya
shigo da allura daga d'akin shi, macen dake
kunyar shi sai gata ta hau waro ido... Sai ya hau
lallashi,kan tai hakuri ba da zafi zai mata ba, kai
ta k'ada, kan a hankali ta tashi, tsinin allurar
kawai taga ta fara yarfe yat'sa. Hmm,tana kai
miki Fure. By Feenat Ja'afar.
Like 路 Reply 路 Report 路 Apr 24
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 24_Soyayya suke kam
kamar babu gobe, a satin su Umma da Ya
Suleiman suka tare a sabon gida, amma fur
mutumin yace ya gano mata gida ita sai tai
wata,sai dai satin ta biyu taje,gida kam yayi,d'uk
da ba wani kato bane amma d'ai ya ninka nasu
na Zaria ma na da,katon parlour yasa aka zana
ma su Umman,ba wani kayan azo mu gani ba
ne,amma tsarin yayi, y'ar TVn su "standard" da
"dish" domin k'allo, kujerun su ma d'ai dai
k'arfi,sai t'sakiya "Chinese carpet",da "tiles" sai
"shining" yake,aciki yai musu "3 bedroom"
Kowanne da bandaki a ciki,da kitchen din Umma,
sai waje yai d'akin su Hassan guda biyu, da
"public toilet" t'sakar gidan y'ar madaidaiciya, ya
zuba musu "interlock". Sosai ajiya tai rana, filin
makotan su Abban Ya Suleiman ya siya,katanga
kawai ta had'a su,sai ya fidda kofar yadda zai
iya zuwa ma kowa. Randa suka tare murna
gunsu ba a cewa komai,dan kam ko yaya sabon
waje ak'wai k'yau. Da ta cika sati biyu ya batta
taje ganin sabon gida,d'uk da shi zuwanshi 2.
Ana haka azumi ya kama, sosai yana taimakon ta
ga kuma Maryam, dan "store" gare shi na delar
magani babba, d'uk da yakan je asibiti jefi-jefi,
amma zuwa shagon yafi,sannan yana da masu
kullar mishi,yanzu burin shi su Hassan su gama
secondary ya d'aura su kai, duk da ko ita FURIIN
bai sanarta ba. An gama azumi lafiya yau ta
kama sallah, t'saye yake gaban "mirror" ya daga
kai tana 6alle mishi ma6allin rigan shi, tana
gamawa ta wuyanshi da hannunta tana
murmushi, sai ya dago jin ta gama, "kai k'yau
sosai.. Ta karasa tana k'allon wuyan, juyarta yai
gaban mirrorn suna k'allon Kansu aciki da
murmushi, sai ta bashi sarka,cikin nutsuwa ya ke
6alla mata,sai ta shafo wuyan ta mudubi tace"
thanks. Murmushi kawai yai tare da d'auro kanshi
a kan kafadarta, fuskarshi ta shafo, "hala yau
azumin magana kake? Murmushi yai tare da kara
juyo ta, "kinyi k'yau ne shi yasa banson kat'se
k'allon ki da magana,ki gane ke d'ai, ya ruko
k'ugunta,sai tai kasa da kai tana murmushi,
idonta ya manna "lips" nashi,yana son yaga tai
d'an kasa da kannan tana murmushi, sai yaga
kamar "eye lashes" nata na karu wa. Hoto yai
musu,kan sukai shirin zuwa masallaci. Ana idar
da sallah ana huduba ta ciro waya tana mishi
"Happy Sallah" sai ga nan nashi, sai tai
murmushi, tare da goge nata tai mishi mai
sanyaya rai ta tura. Yau wanda bata ta6a gani
bama a abokanshi sunzo k'wasar gara, Furiin shi
abar alfaharin shi ce wajen girki,shi yasa ba
musu ya barta ta cigaba da makarantar ta. Tana
daga kitchen ita da Maryam,suna jiyo santin
su,sai kara fasa mishi kai suke, bak'in nan har
k'unne, Furii ta fitarshi kunyar Abincin sallah.
Washegari tai ma su Mama da Umma lafiyayye
su ma, "flask" daban tai wa Momy, Mama ma
haka. Lokacin suna parlour Abba yana ta fad'an
jiya basui abinci ba, yauma da yunwa zasu
barshi? Sam ya t'sani abincin y'ar aiki,yar aiki
mai girkin taje hutun sallah,ga Momyn ce da girki
tun jiya,nufin shi tashi yai bangaren Mama sai ga
nan flask daga Fure, shak'e da sinasir da wata
hadaddiyar miya, taji kaji,da murmushi Abban ya
k'alleshi, lokacin da yake gaida su, a gaban
Momy ya ajiye k'wandon. Da fara'a Abban yace
mishi "mey muka samu ne Abba na? Baki Momy
ta ta6e, sai yai murmushi, "Abba abincin sallah
akace na kawo muku.. Da fara'a ya k'alli Momy,
"Maryam bani,zuban naci anan ma,dan fita zanyi,
yai nufi kan "dining room'' d'inta. Ba dan ta so ba
ta d'au k'wandon tai kan "table'' d'in, tana bud'e
"flaks" kamshi ya doki hancin su,tuni Abba ya
fara tattare hannun rigar shi, Ahmad dake gefe
ya girgiza kai yana murmushi, sai yai "kitchen"
d'in Momyn ya tarowa Abba ruwan wankin
hannu. Zai fito sai ga nan momy,itama shi zata
d'ebo,harara ta sau mishi kan tai hanyar d'aki
dan jin haushin zag'wadin uba da d'an akan
abincin Fure. A kusa da Abban ya zauna,sai wani
lumshe ido Abban yake yana k'wararo santi.
Shikam gogan abin nema ya samu, yasan ko
waye in yaci abincin Fure sai yai santi. "Baba na,
da murmushi Ahmad d'in yace "Na'am Abba, sai
da ya kara yankar sinasir ya d'ang'wala a miya
kan yace, "amma makarantar koyan girki iyalin ka
take.... Haba wa,mai Ahmad zai in ba dariya ba,
Abban yace"Allah kuwa,, dake Abba cikin yaran
shi Aboki yake zamar musu. Kan ya farga yaci
tayi biyar, kira yake abarnan kamar an sa mata
madara. Shidai Ahmad baki yaki rufuwa. Tare
suka fito da Abban, shi yai mota,shi kuma ya nufi
bangaren su Mama. Yau ita kad'ai ce, Ummi d'uk
sun fita dasu Rukayya. Kok'arin tashi take ta
d'aura girki sai ga nan sallamar Ahmad d'in. Suna
gaisawa yace ga nan abincin inji pretty, cike da
jin dad'i ta bud'e tana godiya. Abinda sirikan
gidan basu ta6a ba kenan, wai kawo abinci ko
abincin sallah, su ganin su bata lokaci ne ma.
Sai ga Fure da bata ma fi wata da sati biyu ba ta
kawo sabon sauyi. Labarin santin Abba yake ba
Mama suna dariya. Tace "nima dama ko'k'arin
tashi nake na d'aura kan yaran nan su dawo.
Sosai Mama ta yaba da zabin d'anta, ganan
yaran nasu da suka taso cikin d'aular ba wacce
zata ma abinci mai dad'i, su d'ai barsu a mai aiki
sai ko dafa indomie. Ita kam Momy su Abba na
fita ta dawo parlourn, d'uk kamshin miyar Fure ta
karad'e mata "parlour", sai ta hau t'saki, da
mamakin ta Alhaji yaci da yawa da ta bud'e,
gashi fa itama ranta ya biya, amma sam taki koh
ta6a miyar. Tana nan a parlourn taji hayaniyar su
Rukayya, kana ganin su kaga sun k'waso gajiya
da yunwa. A kan abincin Rukayya ta
sauka,Huwaila ta zauna kusa da Momy, tana kai
loma d'aya ta hau lumshe ido, taji abinci ba irin
na Iyabo mai aiki ba. "Kai,"delicious".. Hannu
baka hannu k'warya ta fara ci,sai ta k'allo
Huwaila, "ka'r kiyi missing.. Da sauri itama tai
kan table d'in, daga t'saye ta d'an dana, a zaton
ta ko ba dad'i, ai tuni ta ja kujera.. Sai da sukai
nak, kamin Rukayya ta k'allo momy wace ta sau
baki tana k'allon su. "Momy yau kin mana mai
dad'i, kai,yaushe rabon da na ci irin wannan
abincin da yawa? T'saki Momyn tai,kan tace
"abincin kishiyar ki toh kika ci, kuma wai dan
iskanci suka hau k'ak'arin amai na gulma.
"Amma d'ai Momy da kin fad'a tun farko wallahi
bazan ci ba, cewar Huwaila, sai sukai kitchen
suna ta bala'i, wai y'ar neman gindin zama,sai
d'ai fa kan a wanke hannu har lashe wa akai
bama su sani ba..y'an Kot'ar nan. By Feenat
Ja'afar.
Like 路 Reply 路 Report 路 Apr 24
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 25_Da ya je gida tai
mamakin yadda taji wai y'an gidan na santin
girkinta,sosai ya ji dad'i, dan murna sama yai da
ita suna hajijiya da tuntsura dariya. Shi yasa
yamma nayi tai wani abin,sannan tasa ya siyo
mata Aya da kayan had'i. Washegari ma
hadadden "meat pie'' da "doughnut" tai musu da
kunun Aya mai sanyi da k'ankara cikin kula,ya ji
K'wak'wa da kayan had'i da madara. Tun jiya da
yamma tai "doughnut", ta nika ayar ta,dake suna
da wuta "standard" ta samu k'ank'ara. Komai
Fure tai tana burgeshi matuka, ga nan kullum
cikin sabon t'sari take na girki. Fitowa tai daga
kitchen jin yana kiranta, da mamakin shi sai yaga
har ta gama shiri cikin "favorite" d'inshi wato
"Orange color". Wani dak'akken "swiss" ne mai
ruwan Orange da filawa fari, sai tai amfani da
wata "fashion" na kalar kayan,shi bai son
kit'so,sai ya had'u da mai son fakin,daga chan
kasan d'aurin tumin nad'in gashinta ya fito,sai ta
ja g'yale saman kan. Sosai tai mishi k'yau dan ta
lakanci abinda yafi so, karasa yai tare da k'ar6ar
abin hannun nata sai ya manne hannunta cikin
k'wanon da nashi, in ta ja sai shima ya ja,sosai
filawar tai k'yau ta hannun. Sai tai murmushi,
ganin hakan sai ya sassauta ta cire hannunta
tare da g'yara g'yalen, k'wanon ya ajiye sai ya
hau tayata g'yaran g'yalen. Ita d'ai nata
murmushi. Suna a mota hannunshi rike da lalle
yana dan dubawa tare da k'allon hanya,ita dariya
ma yake bata, dan tun safe da ya fita sauke
kayan "storen" shi da aka kawo bai dawo ba sai
dazun,shima yana wanka ya kara fita,sai waya da
ya mata gashi nan zuwa.. Sai zuwa yai yaga
lalle,mai yi har ta tafi, kuma ya kasa tambayar
yaushe akayi. Har suka je gidan suna a farin ciki,
sosai kamar wani rakumi,haka yake zama in yana
gaban Prettyn shi. "Part" d'in Mama suka sauka.
Ko jumawa batai ba tace taje wajen Momy,har
ga Allah tafi kaunar ganinta da Mama. Nata
"snacks" d'in ta ajiye Ummi ta d'au d'ayan sukai
"part" d'in Momy Gomnati. Kusan ilahirin gidan
da sirikansu a gidan ta same su,Aunty JIDDA ce
kawai bata a cikin su,harda amarya Hassana da
aka dawo daga "Honeymoon" ana ganinta aka
hau fikara. Har kasa ta gaida Momy,a ciki-ciki ta
amsa,daga nan kala bata kara ce mata ba tai
d'aki. Wajen y'an parlourn tai yo,bayan ta zauna
ta gaida su,d'uk sun amsa,amma biyu kam keya
ma suka juya mata. Aunty A'i ce tai mata
magana kan daga zuwa d'aya shiru, sai tai kasa
da kai tana murmushi,kan ta dago, "zamu zo
InshaAllah, Aunty Maryam ke harar su Sa'a,kan
su saita k'allon sun, sai suka d'an basar. Har
kusan azahar kan Momy ta dawo "parlourn''
samu tai suna alfari ma Fure, d'an t'sabar cin
fuska wai tarihin kanshi kowa zai bayar tunda an
hallara yau, kowa yasan juna, ita d'ai Aunty A'i ta
hakimce K'afa d'aya kan d'aya a kujera tana
d'anna waya,dan sam bata shiga haukar nan ta
k'annen mijinta. Amma jin Bayanin da Huwaila
take,kawai sai ta sau baki tana k'allon su da
mamaki. A ranta tana"Oh,thank God, Allah ya
gama su da sarakan dagawa da nuna su sune,
sai ta k'alli Momy,ko ajikinta, asalima murmushi
take musu ana k'wada arzikin gidan su. "Ni suna
na Sa'adatu.. (Huwaila) in bracket. "Ina da
aure,da yaro na d'aya, ta shafa ciki, "sannan ga
nan na biyu. Har wani k'ada ido take, "Abban mu
ya mallaki gida je har ba adadi,sannan kud'i a
"accounts" bamu san adadin shi ba,ga motoci sai
wanda ka kaga damar hawa, kowacce acikin mu
yakan mallaka mata mota in zatai aure,da gidan
ta na kanta,sannan mu fita kasar da muke so in
hutu ya t'saya, kai,kud'i yayi a rayuwa. Ta fad'i
tana k'allon Fure da ta sau baki. Sai ta k'allo
Hassana, " ke fa Matar yaya? Hassana ta g'yara
zama, tare da y'atsina, "ni baba na d'an Kasuwa
ne,sannan d'an siyasa ne ajahar nan da ma
Arewacin kasar nan,sannan yana aiki da
"Government'' nima ban san adadin kud'in da ya
tara ba,Abu d'aya na sani,shi sananne ne acikin
masu kud'in jahar nan. "Ga nan kuma t'sarabar
"Honeymoon" ta karasa magana tana wani k'ada
kai da shafa ciki kamar wacce tai abin kirki. Ita
d'ai Fure tai kasa da kai,abin har ya d'aina bata
mamaki, ya dawo bata dariya. Huwaila ce ta
k'allo ta, "Amarya ke fa? Dagowa tai tana k'allon
irin y'atsinar da mai tambayar take mata. Sai tai
murmushi, Ahmad da tun zuwanshi yai tsaye a
"corridorn" Momyn, har zai shigo,sai ya t'sinkayi
maganar Furen tana ce musu, "Ni? Sai suka daga
Kansu wasu harda murmushin keta. Su a dole
zasu tozarta ta. Sai tai murmushi kan ta k'alli
wani gefe. "Furera muh'd suna na. Baki suka
ta6e harda tafawa,wai "Furera"?? Sai tai
murmushi tace "Baba na makanike ne shi,mai
g'yaran mota ko babur.. "bai da kadara,sai
rumfar aikin shi guda biyu. Sannan ba fittacce
bane a garin nan balle ma akasar nan. "Tabbas!
ban tunanin yana ma da "account" ma,balle
kud'in shi har ya gaza kididdiga, sannan ko gidan
kanmu bammu dashi,a haya muke zaune,sai dai
Hamdala ga Rabba, abu d'aya na sani... "Baban
mu zaki ne,mai nema da k'arfin shi da Allah ya
bashi domin yaran shi, sannan ya bamu ilimi
wanda zai taimake mu anan duniya da kiyama, ya
bamu farin ciki, wanda har kullum in mun
k'alleshi mukan ce Alhamdulillah. "Sannan ya
bamu..... "Ke!!! ya ishe mu haka, kai ta dago,
Momy ce ta kat'se ta, sai sauran y'an parlourn
suka sa mata dariya,banda Aunty A'I da Aunty
Maryam, wanda tunda ta fara suka nutsu
sauraren ta jiki a sanyaye, tuni farad d'aya ta
k'wanta musu a rai,ita kam Ummi d'an karamin
t'saki tai ma su Rukaiyyan.. tana jin Rukayya
tace "Rubbish" cikin y'atsina. Sai ta k'ada kai,
tare da yin kasa da kai tana murmushi tare da
wasa da y'atsunta. Kai ya jingina a jikin
bango,t'sabar So da kaunar Furii ke kara shigar
shi, tabbas ya t'sani fari'a, sosai ta kara kima a
idon shi, d'an fed'e musu ainashin ita wacece...
Ji yai an dafa shi, da sauri ya bud'e ido ya k'alli
gun, Mama ce,har da d'an guntun hawayen ta
dan tun t'sayuwar shi ta t'sinkayi komai, sai ta
k'ada mishi kai, tare da ruko hannunshi suyi
"part" d'inta. Zama sukai,sai yai jugum, itama
d'ai shiru tai, chan ta kira shi ya dago,da
mamakinta sai taga idonshi ya k'ada kamar zai
kuka, sai ya marairaice mata, kafadarshi ta dafa,
"Ahmad, kai hakuri,ni ina ji a jikina matarka
alkairi ce gare mu a gidan nan, dole kaji ka toshe
k'unne ka, dan nasan zata iya bawa kowa
amasarshi d'ai d'ai shi tunda ta bada a wannan
karan, ,kar ka fara tunanin cire ta a y'an uwan
ka..kai hakuri, da sannu zasu gane nasan
wataran. Kai ya k'ada mata. By Feenat Ja'afar.
庐NWA. Feenat.mywapblog.com
9/29/16, 2:31 AM - Queen Safiyyert馃憫: Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 26_Ko minti biyar basui
da dawowa ba sai gasu ita da Ummi da Aunty
A'i. Fira suke cikin murmushi, sai Momyn ta dan
ji dad'in yadda Aunty A'in ta sau ma Fure jiki.
Aunty A'i tace, "dan d'aki ashe tare kuke da
amarya? Kai ya k'ada mata yana k'allon Furen da
murmushi. Sai mama tace Ummi ta zuba musu
doughnut dasu kunnun Ayar, sai tai ciki dan basu
gu,cikin murna tai kitchen da zamud'in zata kara
cin abincin Fure. K'allota Aunty tai tana taunar
"doughnut", "wai gaske ke ne ki kai ba aikatau
ba? Murmushi tai kan ta dan k'alli wajen
Ahmad,itama Aunty A'in sai ta k'alleshi. "Ok,kai
kayi kenan? Kai ya k'ada, "ya kika ji toh? Kai ta
k'ada tare da dauk'ar "meat pie", wannan ma ta
hau k'ada kai cikin santi, sai d'ai Ummi na zuba
mata kunun Aya ta hau g'yara zama, fad'i take
"kai,wannan kuma mey ne? Dariya suka hau
mata,ita kam ta dage da gaske take bata san
kunnun Aya ba,ita d'ai Fure kawai murmushi take
musu, dan tasan tsaf sai ta kasa sannin, dan
y'an gayu sai da lemon k'wali. Suma achan ba ko
kunya suna ganin Aunty Maryam ta fara ci suka
zira hannu, barin Hassana,kamar wacce bata
taba ganin filawa ba haka take narkar "snacks"
d'in. Rukayya ce bata ta6a ba,tabi Momy suka
zuba musu na mujiya kawai. Amma chan kasan
ranta bata manta daddadan abincin Fure ba.
Suna gamawa sukai bangaren mama,sai d'ai
yadda Aunty A'i ta had'e rai,shine yasa suka
gagara tankawa Fure. Sai da akazo sallah tukun
ta yaye g'yale da nufin zuwa alwala, baki Ummi
ta saka ita da sauran,ganin gashin Fure,ga nan
ilahirin shape nata ya baiyana cikin les din. Sai
tai murmushi, tana jiyo musun Huwaila da da
Hassana kan wai "attachment" tasa. Kawai sai ta
k'ada kai ta shige alwala. Har ta iddar ba wanda
ya motsa sai Ummi, Aunty A'i tace tana fashi,
Aunty Maryam kuma tana gun mama, kawai sai
ta zuba musu ido, da mamakin ta har uku suna
kan waya ana nuna kayan k'arya na d'aki wai
Huwaila zata sauya. Mama ce ta fito,sanyin hali
yasa ta tambaye su tukun sunyi sallah? Kansu na
waya suka girgiza halamar A'a, sai ta had'e rai,
''toh maza ku bar min nan, ace d'an musulmi har
uku bai sallah ba? Fure d'ai ikon Allah take
gani,ba musu suka bar parlourn sukai na
Momy,sai Hassana ce ke sinke kataje tai alwala.
Sam basu kaunar zama kusa da Mama,ita sam
bazata bar bawa ya wataya ba,ga nan Momy,suci
karan su ba babbaka ma ba ruwanta dasu.
Washegari kuma tai gidan su,sai dare ya d'akko
ta suka dawo. Sai dai koh a fuska har yau bata
nuna mishi abinda y'an uwanshi suka mata ba.
Sai d'ai a ranta tana fad'in ta d'aina tanka
musu,dan ta san rashin islamiya ke damun su.
Sai d'ai Hassana tafi bata dariya,mai tunkaho da
kud'in ubanta. Kud'in Tukudi, kud'in cizo,kusan
unguwar su d'aya da Y'an uwan su Adama, ta
bata sirrin komai ai, karya kuma ta kare. Tun
daga wannan ranar d'uk "weekend" d'in duniya
sai Fure ta aika ma Abba dasu Mama abinci,na
satin nan sai ya ninka na satin gaba dad'i. Sai ya
zama har Allah-Allah Abba yake ya ji ance
"weekend " tayi yana gida,dan ya k'washi garar
abincin sirikarshi mama na gefe tana mishi
murmushi. Dan sam Momy ta d'aina k'ar6a koh
an kawo mata. Ko ran girkin Momy ne kuwa indai
ya fad'a a ranar kawo abincin Fure Abba shi zai
ci. Bashi ba,hatta sauran mazan gidan irin su
mijin Hassana nasan girkin Fure. Dan ak'wai
lokacin da yazo ya samu Fure ta gama girki tana
"serving" yayan shi shima ta zuba mishi, da
hadd'en lemonta na kullum,tuni ya soma wa
Ahmad santi, nan tana daga d'aki taji yana
t'surkutawa Ahmad d'in wallahi ba abinda
Hassana ta iya sai dafa indomie da k'wai,kai
ranar Fure taci dariya ta gode Allah. Sosai zata
gode ma Allah a bisa yadda ya sauya rayuwarta
farad d'aya.. Babban farin cikin kuwa shine
yadda ta zama fitilar haskawa ga mijinta, ta
zama abar alfarin shi, ya zama abin nuna ma
sa'a, domin ya bata d'ukkan farin cikin dake a
gidan aure,ance zo mu zauna zo mu sa6a.. Toh
a gaskiya Fure sai anyi kure,kan taga sun sa6a
d'in, albarkacin mijinta ta leka garin manzo, ta
leka kasar da ko a mafarki batai tunanin zuwa
ba. Sai d'ai dake Allah ya kan jarrabi bawanshi a
d'uk farin ciki toh dole ak'wai bak'in ciki, ba
komai zaya had'a maka 100% ba a
rayuwa,matuka yanzu burinta haihuwa. Ko dan
ganin yadda har ta fara taka matakin gori daga
y'in shekara agun dangin Ahmad. Yanzun kam ta
kara samun matsayi, daga y'ar MATSIYATa ta
koma JUYA. Bata jin da taron da za ai a watse
lafiya ba tare da an wat'sa mata magana ba.
Hakan yasa ta halarci ganin likita,ko d'an ganin
mey matsalar. Duk da shi ta gun Ahmad d'in d'uk
kaunar shi da yara bata ga chanji ba, asalima
cewa yai yaushe ma akai auren? Kar ta tada
hankalinta, "soon'' zasu samu baby. Tanan kawai
takanji sanyi,har ta manta bakin cikin su
Huwaila. Ranar sun fito ziyara sukai har gidan
k'aninshi mijin Hassana, dak'yar ya yarda,shima
sai da tace bai fa je ganin baby ba. Suna a
"parlour" yana cin abinci, da murna ya tari d'an
uwanshi, itama Hassana ba laifi, ganin Ahmad ta
sau mutunci,dan sam bai bata fuska koh a gida
suka had'u. Sai dai motsi kad'an ta ambaci
sunan y'arta, ita a dole zata bawa mara D'a
haushi. Murmushi kawai Furen ke mata,shikam
Ahmad kamar an tsikare shi yace ta tashi su tafi.
Direct gidan Aunty Jidda suka sauka, hakima
isassa, Allah ya gani d'uk Familyn su Ahmad tafi
ganin tsanarta karara akan Fuskar Aunty Jidda.
Ba abinda ta bari na Momy,sosai in ka ganta sai
ka d'auka K'anwar Momyn ce ma,dan sosai tafi
Momyn tsufa. A kofa ya batta kan zai shigo Abba
na neman shi. Kai ta k'ada mishi, sai d'ai tana jin
jina shigarta gidan ita kad'ai. Rukayya da Huwaila
k'wa suna gidan,uku ta had'u mata. Tun daga
gaisuwa ta d'auke suka d'auke mata wuta,Aunty
Jidda ta had'e ran nan. A walakance Aunty Jidda
ta k'alleta ta wat'sar, sai k'alli su Rukayya,
"nikam ku tambayi Matar Yayan naku naga har
yanzu shiru,sai ban ruwa muke shuka na hau
hawa.. Baki Huwaila ta ta6e, "bari dai kiji ta
bak'inta Aunty, sai ta k'allo Fure wacce itama su
take k'allo cike da mamaki. Sai tai kasa da kai
tana murmushi. Tamkar wata Umman ta tace
"Wai ke har yanzu shiru ne Fure? Sai Rukayya ta
amshe, "Ki ka sani? Kila d'ai "JUYA" ce...Da
sauri ta k'allosu fuska d'auke da mamaki,kan ta
koma kan Aunty Jidda, baki ta ta6e,sai ta tashi
ta basu gu, su kam ko ajikinsu, asalima dariya
suka hau mata harda tafawa,, kamar kullum,yau
ma ta kasa tanka komai a game da maganar da
ake ya6a mata d'uk a rashin bata haihu ba cikin
shekara d'aya. D'uk da tasan tana da damar
ramawar a kansu, maimakon hakan ma,sai kawai
ta kara kasa tare da k'adashi tana murmushi. By
Feenat Ja'afar.
Like 路 Reply 路 Report 路 Apr 25
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 27_Sosai tana
mamakin d'uk bak'inta da iya bada amsa a
zance, amma in an kira ta da "JUYA" sai tai
shiru. Ba shak'ka kila wataran Allah zai ara mata
rana ne acikin ranakun rayuwarta d'an zuwan
hakan.. Ko kuma baya rasa nasaba da ganin
darajar mijinta, wato Habeebinta Ahmad dake
d'an uwan su. "Kinga ai tai shiru, anzo an bake
gida,ana hura hanci anji sanyin AC,baki Huwaila
ta ta6e, "wallahi nafi jin haushin Yaya da ya
k'waso ma kanshi alakakai, k'alleki fa
Rukky,wallahi ke ki kafi da cewa da wannan
gidan ba ita ba,tuni suka hau zaginta cikin
turanci kamar kullum a nufin y'ar talaka ina zata
samu ma "foundation" mai k'yau bare ta iya
turanci. Sosai take nuna musu dolancinta, sai tai
tamkar bata jin mey suke fad'i, ko turanci aka
mata azance sai ta nemi su fassara maata. A
haka har Huwaila ta shigo ma da Rukky maganar
mijinta,kan ta kasa gane inda ya dosa,har ta gaji
da kai karar shi gun Abba. Fure na jin lokacin da
tace ta fad'ashi da Ya Ahmad, tunda k'aninshi
abokinshi ne. A ranta tai dariya har ta gode
Allah, ace y'ar mai dashi ta rasa gane kan Miji?.
Sannan k'warai in bata manta ba ta ta6a jin ance
Aunty Jidda har suka rabu da mijinta bata haihu
ba agun Ummi,toh wai shin g'wanau baya jin
warin jikinsa shi sai na wani? Ko kuma ji nai
batai ba yaran na gun Abban su? Da wannan
tunanin har Ahmad yazo suka je gidan Aunty
Maryam, ita kam maganar bak'inta ma gagarar ta
take,bare Furen ta gane inda ta dosa. Wasa
wasa Fure har ta k'ware a auna kanta da kanta
da pt,ko k'wana d'aya "period" nata yai "due''
yanzun zata d'au "strip", dan tun yana kawo mata
d'ai d'ai yanzu k'wali ya dire mata,shi d'ai kullum
burin shi ta ma d'aina g'wadi, takan k'alleshi da
mamaki,ita ya dace tai mishi lallashi,dan sosai
tana ganin yadda yake son yara koda in su
Adama sunzo mata. Tuni ta kammala makaranta
tun wata uku da suka wuce,ba wanda yasan tana
zuwa,daga Umma sai ummi,fatan ta "result'' ya
fito,yaya yayi alkawarin kama mata shago kan ya
tara kud'in bud'e mata karamin "Restaurant".
Magana ta kara karuwa ne lokacin da Hassana ta
kara samun ciki, sosai take d'anne ranta,har bata
kaunar abu ya had'a su zama waje daya, a gun
mama da Ummi kawai take samun sa'ida. Momy
kuwa, shekara biyu na cika ta tada ballin dole
Ahmad ya kara aure da Rukayya, tunda ga nan
yadda Matarshin tazo. Ko kad'an bai fara gigin
bari Fure taji zancen nan ba,shi yasa kawai yake
bin Momyn da toh, dan ganin Abba ma baice
komai ba. Ita d'ai taga fallin Rukky ya karu,
sannan Momy ta rage mata wani abin, maimakon
haka ma,sai ta t'siro da mata murmushi in tana
gaida ta ko in ta ganta, wanda kai kana gani
kasan mugunta ne. Allah sarki Fure baiwa ta
Allah. ************************ Doguwar ajiyar
zuciya ta sauke,lokacin da ta gama tuna baya,
tuni sai ta tashi ganin lokacin sallar "Duha" yayi,
yi take tana kai ku kanta gurin Allah, in har tana
da rabo na alkairi toh Allah ya bata. Harda dan
guntun hawayenta dan tuno da jiya a gun sunan
Hassana. Sai ta samu kanta da daga hannu, tana
mai rokon Allah indai tana da rabo na haihuwa a
gaba,toh dan t'sarkin mulkinshi ya aramata rana,
ya ara mata lokacin zata had'a kan kowa dan
bashi sakamakon abinda ya tusa mata. Tana
shafawa ta hau kuka, sai da tai mai isarta kamin
tai shiru taje ta k'wanta. "Text" tai ma AAAn ta
kamar yadda ta saba in tafiya shi da Abba sukai
bata kira. Sai ta kashe waya kan ta juya dan
rama baccin ta. Saukar su kenan ya kai Abba
gun taron da suka je yaji shigowar "text". D'aki
ya kama musu shida Abba "Hotel" kan yai wanka
yai "ordern" abinci. Chokali yasa yana jujjuwa
abincin yana tuna wa da "delicious" na Prettyn
shi, sai yai murmushi k'ada kai, Furii kam
"special" ce agun shi. Sai d'ai yana mamakin yau
har ya sauka baiji "text message" nata na "safe
journey" ba, hannu ya kai dan tunawa da sakon
da ya shigo wayan shi dazun. Baki ya wage
ganin ita d'in ce kuwa k'wace kan "screen'' an sa
Pretty. Cikin zumudi ya bud'e sakon fuska d'auke
da murmushi. Ajiyar zuciya ya sau, kawai sai
tuno da ta jaka kamar kullum, da sauri ya tashi
ya zuge jakar,sai ga nan abu cikin duguwar ruba
marar kauri nad'e a "wrapping paper". Yana dago
shi sai ga nan wani y'ar "paper", ajiye na hannun
nashi yai, da "pencil" ta "heart" tai "shedding"
nashi g'wanin k'yau, kan a ciki tai wasu mit'si-
mit'sin rubutu. "Ticking beats my heart, and the
desire to see the person that I love. I wish the
best for you in this journey, and I wish you a
speedy return.... Love you. Zame wa yai a
hankali yai k'wanta a gadon, yana mai shafa jikin
y'ar guntuwar takadar. A hankali ya mike,sai ya
ware wannan bowl d'in, cikin sauri ya fara ci,tuni
ya k'auda wanda yai "order" tare da jawo wayan
shi da zummar kiranta ya ji "switch up",a haka
yana ci yana kara k'allon heart d'in yaci kusan
rabi,ya kora da lemo. Ji yake kamar yai fuffuke
yaje ga FURIIN shi. A kullum ta duniya yana
alfahari da zaman Pretty mata a gare shi, sosai
ya sani ko a haka Allah ya barshi ya kaunace
shi, balle zai so yaga yaran shi da Pretty kad'ai a
duniya,badan bai san yadda hali zai yi ba,da sai
yace daga kan Pretty ya dat'se aure, hmm,wa
yaga "MIJIN MACE D'AYA na sis (Rufaida Omar).
Sai d'ai yasan K'ADDARAR shi ba a hannunshi
take ba,kawai d'ai "hope" ne. Lalle Fure kin ciri
tutar zama "MAR'ATTUS SALIHA",, wace
k'allonta ke sanya miji a farin ciki,wace rashin ta
a kusan shi ke sashi k'ewar ina ma tana kusa..
Wace ya yabe ta g'wana ce gun iya girki, sannan
k'wararriya gurin iya lafazi mai k'yau da ma'ana.
Tuni shima ya hau t'sara mata nashi salon,yasan
bacci kad'ai ke sa Pretty kashe waya,burin shi in
ta tashi ta bud'e ido da "hot message" nashi gare
ta. By Feenat
9/29/16, 2:36 AM - Queen Safiyyert馃憫: [4/26, 7:41 PM] Feenat Ja'afar.: "JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
28_Sai kusan d'aya ta tashi,warai taji ta,a hankali
ta sako kafarta kasan gadon ta zura ta kalmin
sosonta na "bedroom"tai kitchen, mai sanyi
tasha,kan ta dawo d'aki ta d'au waya,tana
bud'ewa kuwa sai ga nan "text" nashi, sosai ya
ware ta cikin nutsuwa, kamar yasan a "mood"
d'in da take a ciki.
Sai da akai azahar kan sai ganan kiranshi.
Cike da murna ta d'auka tare da sallama.
"Y'an mata na ta tashi lafiya? Dariya ta sau mishi
cikin wata siga, tasan an so tsokana, kan taja
numfashi ta sauke,tsaf a k'unnenshi, tuni ta kara
narkar da murya,
"lafiya d'an samari na,"hope" kun sauka lafiya?
Shiru yai mata kan ya juyo, "lafiya,sai k'ewar ki,,
mey kike yanzun? Numfashin ta kara ja,kan tace
"k'ewar ka nake nima, sai kam ya ji dad'i, nan
suka cigaba da lalacewa cikin birnin su na su
kad'ai.
Kan su farga kusan 1hr suna a manne da wayar
juna.
Gida yace ta d'akko koh Maryam ne,dan Abba
har la'asar bai dawo ba,harda da d'an kukan
shag'wabarta, tuni ya hau lallashi kan yau ne
kawai.
A gida ta samu su Aisha,Adama ma sai gata ita
da yaronta kalil dan shekara 2,ganan tsohon ciki,
sai ta hau mata tsiya,
"A Yarinya,yi a hankali,in dai labor room ne tana
jiranki, kai tai kasa dashi, an tabo mata inda ke
mata kai kayi, Aisha ta k'allo ta," wai Furera ni
har yau kina sa zancen mutanan nan a ranki?
Baki Adama ta ta6e, "wallahi Aisha har mamakin
Pretty nake, wannan kananan kadagarun wallahi
in ni ce tuni an shani na warke,, dan ba wacce ta
isa takani na k'yale.
Murmushi tai, "bazaku gane ba ne ba Ada, ak'wai
ranar tankawar, tana nan zuwa.
K'wafa Adan tai, "amma kinsan nafi mamakin
yadda kika bar Hassana nacin tuwo a kanki? Ke
da kike da abin fad'i ahannu? Ki sau mata d'aya
kiga yadda bak'inta zaya rufe malama, ita da
miki gori wallahi har abada.
"Y'ar gidan tsohon najadu kawai.. Dariya suka
sau, "shege Adama,au Aunty,labari na tsoron ki,
kai Adan ta k'ada, "ai ni tun ranar Dinnern ku naji
komai gun Hanna.
Yau sirrin da Fure bata sani bama na gidan su
Hassana ta sani ka'f.
Sai dare ta d'au Maryam Ya Suleiman ya sauke
su.
Waya suke da AAAn ta tana d'an k'allon Maryam
itama dake waya tana d'an y'atsine wa kamar an
mata dole.
Data gama ta k'allota itama ta gama, "Oh ni
kam, Maryam anya bakki Aljanu? Baki Maryam
d'in ta ta6e, "Kila toh, sai Furen tai murmushi, ''ni
d'ai ki rufawa kanki asiri ki bar ruwan ido,kowa
yazo kice bai miki ba, tashi Maryam d'in tai tana
rage kayanta, kan ta hawo gadon, "ni fa bakar
k'arya ce ban so, wai fa in munyi aure d'uk
bayan sati zaina fita dani waje,mota sai wacce
na ga dama, hala k'aruna ne uban shin.. Dariya
Fure ta hau,kan tace "Allah shirye ki,tace "yoo
Allah kuwa,in gani a kasa man,ko katin dubu bai
ta6a turan ba.
Ita d'ai tana ta dariyar yadda Maryam ke zage
samarinta, ka'f ciki babu g'wanin ta.
Washegari da t'ar6ar Oga suka tashi, sosai take
yaba zafin naman Maryam, d'uk da d'ai ita ke
binta,t'sakanin su shekara biyu ne, Umma
takance Maryam guntun Fure tasha,dan ita harda
taso fin Fure a iyayi da rashin barin ta k'wana.
Matsalar d'aya ita tafi zama a Zaria, dan da sosai
zata k'ar6a ma Fure y'anci.
Kusan biyar d'in yamma sai gasu sun shigo shida
Mohammad mijin Hassana mey bin Ahmad, Fure
na d'aki sai Maryam dake kan dining tana ajiye
ruwan wanke hannu.
Da fara'a tai mishi sannu da zuwa,kan ta dire kan
mai cewa "Matar yaya mey aka mana ne? A
dirare take K'allonshi, Ahmad na kula dasu,sai ya
k'ada kai yai ciki.
Shikam k'allonta yake ganin wannan tafi Fure
fari,tsayi,jiki,da kuma k'yau. Ita kam ina wuni
kawai tace,sai ga nan Fure da fara'ar ta, ganin
irin k'allon da Moh'd kema Maryam yasa ta k'ada
kai, "a Abban Jidda tare ku ke? Da d'an wayan
ce yace eh,sai kuma ya d'an saci k'allon Maryam
dake ko'k'arin cire chargy, "yau,nifa tafiya
zanyi,ai ya dawo, Umm,sai ya ji har muryar su
d'aya da Fure, " toh ki jirani, sai ta dawo kan
Moh'd, "Abban Jidda zauna kan nazo,yau kam
mutuminka ne. Sai ta koma d'aki gun mijinta
tana mai ina ma ina ma..
Maryam na ganin haka ita tai d'akin
bak'i dan kimtsa kayanta sannan da gujewa
k'allon Moh'd.
Sai da ta jiyo hayaniyar su ta fito rataye da jaka
tana yafa g'yale, dan tsaf in ba haka tai ba yanzu
zasu ce sai ta kara k'wana.
Da murmushi Ahmad ya k'allota, "madam
kenan,kamar muna koranki haka? Fure ta k'alla,
kan tace"ai na muku, g'wara na tafi gun Umma
ta.
Ta sauke kan mutuminta,karan nan suna had'a
ido sai yai kasa da kai da murmushi yana d'anna
waya, sai ta d'auke kai tare da dan ta6e baki.
Sudai su Fure na ganin ikon Allah.
Dak'yar Ahmad yasa ta kara k'wana, harda d'an
bubbuga kafa kan bata so hakan ba, "eh munji,
kawo jakar, Fure ta k'ar6a takai d'aki.
Ba sai ga mutuminka ya dawo Washegari ba, tun
goma sai gashi sun shigo shida yayan nashi wai
daga "jogging" yake bayan da mota yazo...Lol.
Ita d'ai Fure sai dariyar ciki take,ta Allah Amin,
wallahi zata so wannan "dramar" dan zatai dad'in
k'allo t'sakanin ta Hassana.
Anan yai break yana d'an k'allon d'akin da
Maryam ta shiga jiya, d'uk Ahmad na kula
dashi,zai so zargin shi ya tabbata,amma kawai
sai ya basar dan ganin iya gudun ruwan shi.
Sai k'wa gashi ya k'allo yayan nashi,"ni yaya
bakuwar ku ta tafi ne? K'allon da Ahmad ke
mishi ne yasa ya hau sosa keya, "no'' ba fa wani
abin bane,,atoh, sai ya d'au tea ya kai baki,bai
zata ba ya ji yayan nashi ya k'walo kiran
Maryam,tuni sai ga Moh'd ya k'ware, dan fa
Maryam ta bashi tsoro jiya da wannan k'allon
nata.
Fitowarta a wanka kenan ta sa kaya, hijab ta zira
ta amsa da d'an k'arfi kan tai waje.
Ganin Moh'd yasa ta d'an kama kai, "Na'am
yaya,tashi Ahmad d'in yai yaja kujera, yana
murmushi ya nuna Moh'd,"ga nan mai kiran
ki,ruwan wankin hannu zaki bashi wai.
Sai ta k'allo Moh'd d'in da yai tsuru tsuru yana
k'allonta. Dariyar shi AAn ya kunshe, ganin zata
tafi yace,"au,ma manta,k'ani na ne fa, mai bi
min,yake tai musu,tace "ina k'wana.
Bata jira mey zai ce ba tai kitchen debo ruwan.
"Haba bros, wallah tsoron yarinyar nan nake fa,
kuma.. Sai yai shiru yana sosa keya, kai yayan
nashi ya k'ada.
Sai ya bashi gu yana dariya jin motsin Maryam
zata fito.
Yanayin da yake ne yaso ya bata dariya,d'uk ya
susuce, ruwan na hannunta ta mika mishi,kawai
sai yai sakare! Yana k'allon ta,kai ta ka'rkatar
tana dan mishi fari cikin murmushi tare da
matsar da ruwan kusan dashi.
Sai ta bashi dariya tare da kai hannu zai wanke
ta d'ang'warar kan table d'in tare da yin gaba
kamar ba ita ba. Kai ya k'ada, shi yasa yace
tsoron ta yake.
A gaskiya Maryam ta mishi,sosai ba k'arya sai
d'ai taya zai fara tunkarar ta da tsoron?
K'wada wa masu gidan kira yai kan shi zai wuce.
Sai ga nan Fure ta fito tana d'an dariya jin mitar
Maryam kan k'allon da Moh'd ke mata.
"A,ka bari ya fito,yanzun,ina zuwa, sai ta nufi
d'akin su.
Kusan a tare suka fito da Maryam, masu gidan
sai y'ar dariya suke,shi yana k'allon Moh'd ita na
k'allon Maryam, "wai mintsinin ki ake ne
maryam,? Baki ta turo, ''nifa tafiya ta zanyi,
kawai ku barni, ta karasa tana dan magana
kamar mai shirin kuka.
Ahmad ya k'ada kai, "toh munji, amma gobe zaki
zo?
Kai k'ada,"nikam gobe zan bar garin,Zaria ma
zan gudu.
Yin duniya taki zama, suna k'allon yadda suke
dan k'allon juna,ita Maryam na basar wa. Moh'd
bai zata ba ya ji Ahmad yace "d'an sauke ta da
Allah Bros, sai ya k'allo Maryam d'in da tai kicin
kicin, sai Ahmad yace," koh zaki bari mu fita
anjima? Da sauri ta k'ada kai, dan tasan yanzu
sai su kara rike ta.
Shikam kamar an mishi gafara yaji, da azama ba
musu ya tashi yana musu sallama.
A mota suna tafe yana murmushi shi d'aya, ji
yake kamar ma ace man Maryam ta zama tashi
ne zai kaita unguwa.
Kanta duk'e ta ce mishi "left" k'allo ta yai, kanta
na waya, sai yai yadda tace, suna dan kara gaba
ta kat'se shi da "right".
Sai yai murmushi, yana son mace mai aji. Da
"left'' right" suka zo inda zai sauke ta.
Da mamakin shi sai yaga ba gidan su Furen
bane,dan rabon shi da gidan tun suna na kasa,da
ta barshi chan zai kaita.
Godiya ta mishi zata fita yace "Maryam, sai ta
juyo tare da tsare shi da ido, sai ya kuma hau
kame kame.
"I thought ke K'anwar Matar yaya ce? Kai ta
k'ada, "K'awarta ce.
Zata kara fita yace, "OK, ok,nan ne gidan ku? Sai
ta kara k'ada kai, "Umm Umm.. Sai ya marairaice
mata, "dan k'watanta min, K'allonshi tai, kan ta
k'ada kai, "a unguwar zana nake,layin y'an kara..
Ido ya waro, zata kara fita yai saurin tsayarta,
"meye zana da kara? A takaice tace mishi
"Unguwa ce.
Bata jira ba tai waje ta barshi baki sake.
Har ta shige gida yana k'allonta.
Da yaje gida kuwa Allah-Allah yake yamma tayi.
Yadda ya dinga k'waliya kai kace gun d'aurin
aurenshi zashi, har Hassana dake K'allonshi ta
kasa jurewa. "Wai Abban Jidda yau ina zuwa
haka da wannan irin d'aukar wankan? Murmushi
yai, ba tare da ya k'alleta ba yace "waje mai
mahimmanci, sai ya juyo, "ke d'ai nayi k'yau?
Baki ta ta6e, kan tai mai banza, shi ko kula da
cikar da take bai ba,burin shi kawai ya isa ga
unguwar Zana layin Y'an kara.
By
Feenat Ja'afar.
[4/27, 12:10 PM] Feenat Ja'afar.: "JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
29_Sukam su Fure tun fitar su tai gun tarairayar
mijinta,sai d'ai tana ga kamar Maryam zata bata
shirin, wallahi har ta gama hasko Maryam a
matsayin kishiyar Hassana, ita d'ai kawai burinta
Allah kai Damo ga Harawa.
T'saye suke gaban madubi tana 6alle mishi
ma6allin rigarshi suna cikin nishad'i.
Sai kamshi yake zubawa.
Hannu ta mika tare da d'akko hula tana kafa
mishi, sai ta d'an mat'sa tana dubanshi tana rike
ha6a, "ummm...MashaAllah.. Murmushi yai,kan
ya tako gareta, "ke ne Mashaallah, sai kara k'yau
kike kullum, ya rukota,''meye sirrin.. Baki ta kai
k'unnenshi ta rad'a mishi a hankali "So da kaunar
ka ne. Murmushi yai, kamar kar ya fita, kawai sai
ya ruk'unk'umo ta yana d'an shinshina wuyanta
tana dariya.
Sallamar Moh'd ce tasa shi dagowa yana k'allon
Furen, "Oh Allah,, waye wannan? Dariya ta sa,
"bari na dubo, sai ya k'ada mata kai "no bari
naga.
A bak'in gado ta zauna tabi shi da k'allo har ya
fita,sai ta sauke nauyayyen ajiyar zuciya, tana
matukar son Uncle d'in ta, sam bata kaunar yai
mata nisa.
Da dariya ya dawo,yana "fito kiga abin mamaki,
yafo g'yale. Cikin azama ta biyo shi.
Muh'd ne yai k'ankane akan kujera. Yana ganinsu
ya g'yara zama. A kujerar mai mutun d'aya suka
zauna suna fuskantar shi,ita na kan hannun
kujerar, haba,shi yasa suke ba shi sha'awa, sam
shi ba'a g'wada mishi soyayya a gida, tuni ya ji
ya kara zumudi akan K'awar Fure.
"Kin ganshi wai Maryam ya karade nema wai bai
same ta ba,shine yazo ki mai dalili..ya karasa
suna dariya, k'allo su yai, gaba d'aya ya gaji
neman wani unguwar zana layin Y'an kara.
"Matar yaya ki taimake ni, da gaske K'awar ki ta
wahalar ni, mai na har ya kare a neman Unguwar
Zana Layin Y'an kara... Dariya sosai ya basu, har
ya soma k'uluwa kuwa.
Dak'yar Fure ta t'sagaita da ta ta, "kai amma
tasha da kai fa, Ahmad ya k'ada kai, "Maryam
ake fad'a maka, sosai "style" nata ke burgeni fa
Allah, , sai suka kara sa dariya.
K'wafa yai,kan ya tsiyaya ruwan dake roba a
dining ya dawo,
"Au,dariya ma na baku ina sanarku abinda K'awar
ku ta min? Kai Fure ta k'ada mishi, tana d'an
ta6a Ahmad kan yai shiru.
Kawai sai ya sa musu ido.
"Maryam K'anwata tace fa,UWA D'AYA(na Aunty
YBK),
"sannan ba wani layin zana ko kara da take, sai
ta k'allo shi, "toh kai wane unguwa ka kaita? Ba
zuciya kuwa ya fad'a mata cikin mamaki, sai ta
kara kunshe dariya, "nan take da zama,iskancin
Maryam ne kawai.
Ahmad yace "toh mey ta ma irin wannan nema
haka bros? Waya ya ciro,"ku ban numbern ta
kawai, daga baya zaku ji komai.
Wasa sukai ta mishi da hankali,har sai da ya fito
6aro 6aro yace shi fa Sonta yake.
Tab,yau ake yinta inji Fure a ranta, lalle lokaci
yayi dazata danawa Hassy Bom, fatan ta Allah
yasa Maryam ta yadda da Moh'd kawai.
Sam bata nuna ma Ahmad murnar ta a fili ba, sai
ma shi ke nuna tashi, tunda muh'd ya biyo sahun
shi.
Wasa wasa kullum sai yazo ma su Fure, dan
Washegari Maryam ta wuce Zaria da zummar
karasa satin ta biyu.
Sai d'ai kusan kullum sai ya kirata a waya kan
wani bawan Allah ne mai kaunar ta Fisabilillahi.
Binshi take a haka, dan Fure ta bata komai "in
details".
Kamar yadda suka saba shawara da Momy in
abin su ya tashi yauma nan Muh'd yaje da kokon
shi, dan mud'in yasan in Momy ta yarda toh
kamar kowa ya yarda da batun karin auren shi.
Sosai yai mamakin Amin cewar Momy a take,sai
d'ai ya boye matar da zai aura jin Momyn na
mishi fad'an kar ya kara jaju6o musu irin su
Hassana.
Dan tuni ta dawo a rakiyar ta, ganin uban Hassyn
bai ya tabuka komai ko ta haihu,a ganinta da ita
da y'ar matsiyata Fure d'uk d'aya.
Sai d'ai yai shiru yana jinta, fad'i take "karan nan
a ni koh AAA a gidan nan, sam ban ta6a cin ka'ro
D'a mai taurin kan Ahmad ba, in banda haka ina
gami t'sakanin waccan kod'dadiyar matar tashi
da Rukky? Kai ya k'ada mata, "Momy babu kam,
sai tai k'wafa, "atoh,ka d'ai za6a ka darje karan
nan,kar ka kara bamu kunya. Kai ya k'ada, yana
mai tunanin randa Momy zata san wa zai yayu6o
musun.
Gida ya koma cike da farin ciki,tana a parlour
yara na ta tsula ihu, amma sam ita ko a jikinta,
cikin fad'a ya fara mitar tabani bazata kula su
ba?
Sai ta ta6e baki tare da sau mar harar haushi,
"tunda kace baza'a d'akko musu "Nanny" ba toh
mey yai ruwanka acikin ihun su? Sunkuwa yai zai
d'au mahma yana k'ada kai, a ranshi yana "kin
kusa gama na kud'in ki.
Sai d'ai yana daga babyn ya kawar da kai, kashi
tai a "pampers" har ya fara fitowa.
Kamar ya rufe ta da duka ya ji, "mey kike ji dashi
ne Hassy? A y'atsine ta k'allo shi, "da akai mey?
Kai ya jijjiga, kan ya komarta ya k'wantar, "kin
kusa gama na kud'in ki, kiyi komai ba komai,
amma ki tabbatar kan na fito kinsan nayi da y'ar
nan. Da harara ta bishi har ya kule, kawai
haushin shi take ji,dan tayi tayi ya sai mata mota
fir yaki, ga nan Fure karamar d'angarta tana
murza mota, shine fa k'wana biyu take sakar
iskanci son rai, a ganinta hakan zai sa ya sai
mata.
Fure ce k'wance ta k'allon kofa lokaci-lokaci, da
halama mai gidan take jira, ga ya manta
wayanshi a gida.
Hannu ta kai kan wayar jin ana kira, "Huwaila"
taga an rubuta, sai ta ajiye taki d'auka har ta
yanke, tunanin dabi'ar Huwailan take a gare ta,
sai ga nan wani kiran ya sake shigowa.
Kamar kar ta d'auka, sai d'ai ta share ta daga da
zummar sanarta baya gidan.
Ba ko sallama ta sau kuka cikin wayar, "Bros dan
Allah ku dawo, gashi nan yana kara kirarin shi
wallahi yara biyu yake son ya tara sai dai nai
"abortion, daga magana har mari na yai.. Furen
naji daga cikin wayar mijin Huwailan na fad'in ta
sanarwa kowa ma, amma shi kam bai san da
wani ciki ba, kuma in aka takurashi zaiyi rashin
mutunci.
Da sauri Huwailan tace "kaji koh Bros, kaji da
k'unnenka... Da sauri Fure ta kat'seta da "za'a
sanarshi in ya iso, sai ta kashe ta bar Huwaila da
baki sake.
Fure cike da mamaki tai t'sam da tunanin fad'an
Huwaila da mijinta, chan AA ya nufa kenan tun
dazun?
Tab,yau ake yinta, yanzu dama irin mugun zaman
da Huwaila take a gidan miji akan haihuwa? Wai
bai son tara yara, kuma harda mari? Shin ina
gatan nata da isar? Lalle ta kara gode Allah,
wasu nan suna nema,gashi ita mai gorin tana
haifa amma mijin bai so, mey kenan akai?
Kai ta kara jinjina mata, kawai sai taji tausayin
ta, dan sosai taci a tausaya,daga mari gaba ai
sai duka.
Tana haka sai ga nan mai gidan ya shigo shida
Mohammad, har yanzun mita yake akan mijin
Huwaila.
Har suka zo k'wanciya yana na nata abu d'aya,
dan tsaf ya nuna musu shifa ga ra'ayin shi. Ga
nan wayar da sukai da Huwaila dazun har marin
ta sanar shi.
Dak'yar Fure ta samu ya dan lafa tana dan
"massaging'' kanshi.
"Allah Pretty mutum wani bai da godiyar Allah
sam, tsam tai tana jinshi, "ki duba wani ya samu
Allah ya k'wace au duk'a, wani koh d'aya bai
samu ba nema yake amma lokaci bai zo ba, sai
shi ne dan t'sabar butulci ma Allah ya bashi
su,sannan yai mishi wadata sannan yace bai so?
Wace iriyar rayuwa ce Furii?
Tsam ta k'wanto kanshi cinyarta cikin nutsuwa
take dan shafa kanshi, "kai hakuri, nasan da
ciwo, amma ka d'auka wannan kad'an daga
dabi'ar dan Adam, kawai adu'a yake nema Allah
ya shirye shi Dear.
Kai ya k'ada, "da k'yar ne,dan fa ra'ayinshi ne na
rashin son tara yara, sam tun farko banso auren
Huwaila da mutumin nan ba, amma fir ta dage ita
sai shi,irin abinda nake hanga mata gaba kenan.
Murmushi tai,kan tace "adu'a zaku mata,Allah
kawo mata sauki.
Kai ya k'ada,"toh Amin.
Har suka k'wanta tunani ne fal a ranta.
Hakan yasa ta kara gode ma Allah,dan ya bata
Ni'ima sosai a rayuwa. Wanda in zata butulce
dan Allah ya tauye mata d'aya batai ma kanta
adalci ba.
Dan tayi imani tafi Huwaila k'wanciyar hankali a
gidan Miji.
By
Feenat Ja'afar.
[4/27, 12:10 PM] Feenat Ja'afar.: "JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
30_Abu kamar wasa maganar Muh'd da Maryam
ta tabbata, dan ko gare ta bata ta6a jin wani
saurayi a rayuwarta ba sai Moh'd, bayan dan jan
ajinta daga baya ta yarde, tuni suka dinke.
Sosai Fure tai matukar Farin ciki da wannan
had'i, zata so ganin yadda Momy zataji wa Muh'd
zai aura, sannan za taso sui ar'ba da Hassy ido
da ido.
Dan fa har anje tambaya, d'uk da Abba yaso da
yaki yarda ganin yaushe ma yayi aure da zai kara
mata? Sannan ga nan sauran yayunshi ba mai
mata biyu.
Yau ne ranar da likitan da take gani yace ta
dawo,d'uk da tasa a ranta daga yau ta bar jelar
asibiti, ga nan Ogan baya gari.
Kamar kullum yau ma ya gama dubata yace
komai "normal" lokaci ne d'ai bai yi ba.
Sai ya bata kan taje tai "blood test", dan shi kam
bai gane ba, gashi tace period nata ya wuce da
k'wana yau goma.
A "lab'' ta zauna rint'se da ido za'a d'au jikinta.
Sosai ta t'sani ganin allura,amma dake abinda rai
ke so ne shi yasa ta yarda.
Auduga ya bata ta d'anne gun yace ta zauna a
chan ta d'an jira.
Kusa da wata mata ta zauna,a hankali taji kamar
matar na shesshekar kuka kanta duk'e. Da
mamaki ta zata ko batta lafiya ne, sai tace mata
"sannu baiwar Allah, kiyi adu'a ki bar kuka.
A hankali matar ta dago,zata fi Furen da shekaru
kusan bak'wai, idonta ya k'ada yai jajir halamar
tai kuka har ta gode Allah.
Sai tai ma Furen murmushi kan ta goge hawaye
wani na kara zubar mata.
Kawai sai ta tashi ta fita da result na "urine test"
a hannu.
Ba'a jima ba ganin an sa ai da sauri suka fidda
ma Furen result.
Ido rufe ta fito, tana mai fatan in ta bud'e taga
"positive".
A d'an gefen "lab'' d'in ta t'saya,matar nan ce
zaune tana cigaba da kukanta, sai ta juya mata
baya tare da bud'e ido, sai ta ware "result",
Da sauri ta rint'se ido sai ga hawaye.
Bata nufa ba taji kuka ya su6uce mata wanda
batasan ma na meye ba, ta kusa minti d'aya kan
ta t'sagaita jin ta kusa da ita tai shiru, sai ta
juyo ta k'alleta, itama Matar ita take k'allo
hawaye na zuba, sai Furen tai mata murmushi
tare da sa bayan hannunta tana goge ido, da
mamakinta sai taga matar itama na murmushi
tare da itama goge hawayenta.
Sai ta taso tazo gun Furen, tare da ce mata "ina
fatan ba matsalar mu d'aya ba y'ar uwa?
Murmushi Furen tai tare da k'ada mata kai, dan
batasan tata matsalar ba.
Hannu matar tasa ta k'ar6i "result'' d'in hannun
Fure ta duba.
Da mamakinta sai taji tai murmushi mai sauti,
wanda agun Fure wani hawayen ne ya kara
saukar mata.
k'allo Furen tai,kan tace, "hala kina gudun a kira
ki da JUYA ne sister? Da sauri Fure ta dago tana
k'allon matar, da mamaki tace "ya akai kika
sani? Murmushi matar tai,kan tace "za kiga likita
ne koh gida zaki? Kai ta girgiza mata, "yace in
"Negative'' ne ba sai na dawo ba.
Kai matar ta k'ada, tare da mika mata nata result
d'in, "Pt=positive" taga, sai ta dago ta k'alli
matar da mamakin toh mey yasa ta kuka bayan
nata ya nuna "positive"?
Hannun Furen ta kamo, "muje,nasan za kiyi
tunanin mey ya sani kuka? Tafiya suke tana
sanarta "nima irin kice da,kullum nazo asibiti
naga "Capital Negative" sai nai hawaye, amma
na yau na daban ne, rakani na kai mishi result
d'in kiga. Ita d'ai Fure binta kawai take,dan sosai
ta kosa taji meye dalilin kukan matar nan.
Da mamakinta likita d'aya suke gani da ita, sai ya
juyo ganin su tare da Fure, tuni sai fara'ar shi ta
karu, zaton shi Furen ta samo "positive" ne.
Sai d'ai yana k'ar6a ya girgiza kai, "madam kiyi
hakuri,ki kara adu'a, kin ga nan y'ar uwarki, in
kinji nata zaki gode Allah ne.
K'allo matar, kawai dan ya hucer mata da zuciya
yasa kullum tazo yake bata "pt'', amma shi yasan
sai wani ikon Allah.
Sai d'ai yana bud'e result da sauri ya d'au "glass"
ya kara dubawa,sai ya k'allo matar fuska d'auke
da mamaki, "madam,
result d'in kine wannan? Kawai maimakon amsa
sai ta kara sakar kuka.
Ita Fure har matar ma ta fara bata haushi, dan a
ganinta abin farin ciki ne wannan ba wai na kuka
ba.
Sai dai jin abin da likita yace yasa ta K'allonshi.
Abin yai matukar d'aure mishi kai ne, har bai san
sanda ya kara k'allon result d'in ba yace"how is
this possible? Tashi yai, kawai yace su biyo shi,
ita kam Fure sai ta bi su.
D'akin"scanning" suka nufa, Fure zata t'saya
yace ta shigo itama, taga ikon Allah.
Ido yasa ma allon "machine d'in scan" d'in yana
k'allo. A hankali ya furta"lalle d'ukkan ya6o ya
kara tabbata ga shugaban halitta.
Take ya tuno da kalmar shi ta "how is this
possible, nan take ya Istigfari ga mahaliccin shi,
take ya kara gaskata k'arfin iko na Allah,domin
gareshi " everything is possible ", gashi cikin
ikonshi yace "KUUm..sannan FAYA KUM
d'in,matar da suka sanar da mijinta cewar bazata
haihu ba gashi Allah gagara misali yai iko nashi
kanta.
Ajiyar zuciya ya sau, kan ya k'allo su, "madam
kinga ikon Allah koh? Mai iko akan d'uk abinda
yaso.. " a gaskiya "case" d'inki shine na biyu da
ya ta6a bani mamaki tun fara aiki na. "Yanzu
kam kuka ya kare miki, 4 good ten years yau
Allah ya nuna ikon shi akan ki, kiyi murna da
godiya ba wai kuka ba.
Kai ta k'ada, ita d'ai Fure ta kasa gane inda suka
suka dosa.
Ta d'ai gane matar shekararta kamar goma ne
bata samu haihuwa ba sai yanzun.
Kan Furen ya dawo, "matar "pharmacy" ki dad'a
hakuri, dan tabbas matar nan ta ishe ni ishara.
"Kisa a ranki in har baki haihu ba Allah ne kawai
bai nufa ba.
Kai kawai ta k'ada mishi, tare da k'allon matar,
sai yai rubuce-rubucen shi da taimakon tambayar
da ya yai mata, da murmushi ya dago, "in har
lissafin nan d'ai-d'ai ne toh cikin nan ya ma shiga
wata na hudu fa,right? Kai ta k'ada mishi, dan
wata hudun shine karshen y'in period nata,d'uk
dama ba wai "regular" bane.
By
Feenat Ja'afar.
[4/27, 1:59 PM] Feenat Ja'afar.: "JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
31_Iyanzun ta d'aina kukan, sai d'ai takan k'alli
Fure da itama kawai k'allon matar take cike da
tambaya.
Sai tai murmushi, d'ai-d'ai wata mota ta k'allo
Fure, "zan so k'warai in kin yarda ki bini in dai ba
mai d'aukar ki
na baki labarina,nayi imani daga yau kin d'aina
wahalar da kanki a asibiti, da daga yau kin d'aina
kula zancen jama'a har yazo suna saki a bak'in
ciki, da na zame miki Aya a rayuwar nan tamu.
Kai Furen ta k'ada, kan ta d'au waya ta buga ma
Ahmad dan neman yardar shi. Mota ta
shiga,halamun ya barta,yayin da matar ma ta
shiga tata, a hanya take binta,har suka t'saya a
d'ai-d'ai wani gida, sai taga ma matar batta nisa
da unguwar su Umma.
"Horn" matar tai aka bud'e musu "gate". Gidan
bai fi rabin nasu Fure a girma ba, suna "parking"
matar ta fito, da murmushi tace ma Fure
"Bissmillah.
Kawai ta rasa dalilin da ya sa ta nacewa matar
d'uk da bawai ta santa ba.
Suna da rufin asiri d'ai d'ai g'warg'wado, ta kama
Fure ruwa da lemo kan ta d'aura musu abinci.
Nan da nan itama taji kawai ta aminta da
Fure,sannan da taimakon jin likita yasanta.
Zama tai kusa da Fure lokacin da ta fito a
kitchen, sai tai mata murmushi, ganin tun dazun
Fure na ta binta da ido,ita so take ta gano inda
cikin ya makale har na wata uku, sam sai ka
zata cikinta ne,dan d'uk yabi jikinta.
"Da farko d'ai sunana Fatima,ina da shekara 29,ni
y'ar Kano ce, aure ya kawo ni nan, k'anin Baban
mu ne kawai na sani a garin nan, sannan a wani
hutu nazo garin nan muka had'u da Salman,Allah
d'ai yai ikon shi har na yarde wa auren shi, sosai
ya nunan so tamkar ba gobe,har hakan yasa na
mance da kad'aicin iyayena, abu d'aya na fara
fuskanta shine sam y'an uwanshi basu son kular
da yake nuna min, a hankali ya rage wasu
abubuwan tun kan aje ko'ina, sai d'ai d'uk da
haka ban nemi komai na rasa ba.
"Abi na biyu da fara fuskanta shine jinkiri na ta
gun haihuwa ta, dan tun ana min abu da kawaici
har ya zamo kiri kiri ake min, wasa wasa har na
shafe shekara uku shiru, dan ko 6ari ban ta6a
ba. Duk da a bangaren Miji na ban samun
matsala sam har na shekara uku.
Mukan je ganin likita d'uk wata ni da Salman,ace
mu g'wada na gargajiya,muyi na rubutun, amma
sam babu cigaba.
A wannan lokaci nayi iya hakuri na naga na fita
harkar y'an bani na iya dangin Salman sai d'ai
sun kaini bango.
"Sai ya zama ina d'ari-d'arin shiga cikin su, dan
d'uk wani zama bazai kare ba sai an gorata min
kan ban haihu ba.
In takaice miki sai da na shekara biyar muna
jelar asibiti ni da Salman.
A wata rana da bazan ta6a manta ta ba munje
ganin likita kamar yadda muka saba,tare da
"result" na "X-Ray" da aka min "HSG" a wajen
mu, shima kuma Salman yazo da abinda za'a
g'wada lafiyar k'wanshi, tashin farko farko likita
ya tabbatar wa da Salman ai d'uk wai "tubes"
sunyi ''blocking". Duk da banyi science ba, amma
na gane maganar shi ta karshe wai "there was
no chance of conceiving naturally Ever... Wai zai
de had'a mu da Ogan shi.
"A time likitan dake dubani yaje karin karatu,
ranar naci kuka na gode Allah, yayin da Salman
ke ta aikin lallashi, ya na iya, kinga d'ai ba wanda
zai kaini damuwa, amma in sanar ki a satin har
gida akazo aka wanke ni ciki da bai, kan na zama
JUYA naki sakar ma mijina mara ya kara aure.
Biyu sai tazo ta had'e min,bani inda zanji sauki
sai agun Allah da gun Salman, dan ko gidan
k'anin Baban mu naje sun dunga fad'in "Allah
sarki Fati,shiru koh? Sai tai murmushi, hakan
yasa suma na rage zuwa gidan sun, dan sosai
suke kara min damuwa.
Har ranar da likita ya dibar mana ta cika banji
Salman yace na shirya muje ga likita ba.
Sai da dare nai mishi magana, d'uk da naga yana
ta cika da bat'sewa. Budar bak'inshi sai yace shi
ba inda zashi.
A lokacin nai mamaki, dan sam bai ta6a min
haka ba, Washegari sai ni naje, da ikon Allah
wannan likitan ya had'a ni da Ogan su, ni d'ai naji
yana mai bayani da turanci kan wai ai min
"laproscopy to "unblocked" my tubes.
A lokacin da ido nake binsu,sai dai suna fad'in
zasu dan min aiki kad'an na t'sure.
Tun daga ranar ban kara bi takansu ba, shima
kuma Salman bai tambaye ni ya akai ba.
I yanzun kam na ma fidda rai ga haihuwa, tunda
sun sanar ni in dai ba'a bud'e ba ba zancen
haihuwa.
Haka na cigaba da toshe kunne na,ranar ana biki
gidan k'annin Baban mu naje, kusan d'uk y'an
uwa sunzo, sosai nai farin ciki a ranar,muka
rankaya gidan amarya, chan kusa da y'ar gidan
k'anin Baban mu naje dan ganin kujerar da take
kai ce kawai da waje.
Da zuwa na dama ta fara ta6e baki, cikin wasa
na kula take watsan magana musamman in naje
gidan ta.
Zama na kenan tai saurin mikewa tana fad'in "a
Fatee kar ki min illah man, d'uk na k'alli y'an
d'akin kowa na sabgar gaban shi, sai nace " mey
kenan hakan yake nufi cikin wasa. Sai yamutsa
fuska, "kinsan cikin ba irin naku bane.. Sai tai
waje ta barni da k'allon bayan ta,sai a sannan ne
na kula da karamin cikin jikinta.
Ranar har nazo gida ina mamakin maganar
Maryam y'ar k'anin Baban mu, tun daga ranar
nasa a raina na dena jin haushin kowa dan ya
kirani da JUYA, tunda ga nan y'ar uwata ma ta
jini ta ya6an magana.
Sosai abin ya t'saye min a rai,har na sanar ma
makociya ta lokacin muna a tsohon gida. Sai ta
sanar ni ak'wai wani Malami ya ta6a yiwa
yayarta aiki irin nawa,a watan ta samu ciki.
Jim nai,zuwa wani lokaci nace zanyi shawara.
Ina fita naji sam abin bai k'wanta min ba,dan in
da abinda da nat'sana bai wuce bin malamai ba.
Wasa wasa har muka shiga shekara ta shida
aure, sam Salman ya sauya, abu kad'an hanci ni,
ba makawa ya fara d'aukar zigar y'an uwan shi
kila.
A satin ne kuma naje gidan su duba Umman shi,
sam ban kawo zan sami y'an uwan shi a gidan
ba.
Kusan sai nace d'aya ce bama y'ar tsama da
ita,sai ko Hajiyan shi.
Tana a k'wance a gado suke ya6an magana, sam
bata hana su, sai d'ai ma ta d'auke kai, shi yasa
na kasa gane inda ta dosa.
Da gan gan d'aya ta k'allo d'aya kamar yadda
suka saba, sai d'aya tace ma d'ayar tana ta
had'a kiba ina zata kai, duk ina kallon su, budar
bak'in ta sai cewa tai "ai ni tawa kibar da dalili,
ba kashi kawai take sau wa ba gidan Miji.
A ranar na kasa hakuri,har na sanarwa d'an
uwansu irin maganganun da suke ya6a min.
Sai tai murmushi ta k'allo Fure tana hawaye.
"Kin san mey yace min? Kai Fure ta k'ada, sai ta
tashi tai kitchen tukun ta dawo.
Har yanzun hawaye na binta, "budar bak'in
Salman sai cewa yai waye bazai so ganin
k'wanshi ba a rayuwa..
A ranar ya tabbatar min da cewar shekarun sa
na ja, a gaskiya zai kara aure dan wai ya min
kara...
Kuka ta fara Fure na lallashi, "wallahi a yadda
nake son Salman in ta gunshi ne wannan
matsalar zan zauna dashi har karshen rayuwa.
Ranar nayi kuka kamar nai mey,dan a fili ya nuna
ya gaji da Gaza wata ta rashin haihuwa.
"Zuciya batta kashi, Washegari na tambayi
unguwa, ba musu ya barni,ban zame ko'ina ba
sai wajen makociya ta, dama kamar tana jira,har
da ita mu kaje gun malamin da yayarta.
Zuwa na farko ya bani turare da layu kan in zan
k'wanta na d'aura layar a mara ta na shafa
turaren,in dai har mun kasance tare da salman
zan samu ciki.
Har yana fad'in wacce ta fini matsala ma ta
haihu bare ni. Hawaye ta goge,halamar abin da
ta tuno bai ba.
By
Feenat Ja'afar.
[4/27, 3:30 PM] Feenat Ja'afar.: "JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
31_Haka ina jin ina gani nai "shirka", dan na
had'a Allah da wanin shi, sam ba yadda zaki ce
wannan mutumin Malami ne ba boka ba.
Ana nan ana nan,har wata na biyu ya kama
shiru,ba ciki ba dalilin shi, har na hakura, sai d'ai
in na tuna da gorin jama'a nakanji k'warin
g'wiwa.
Haka na nad'a muka koma wajen bokan nan chan
bayan gari, tuni sai ya fara sirkulen shi, kan ya
k'allo ni yana fad'in dole sai an min babban aiki,
ba musu nace na yarda,duk ban san meye
babban aikin ba,ni d'ai burina na fita sahun JUYA.
Turare ya kaini wani d'aki ya banka min, d'uk sai
da yasa na cire kaya na gaba d'aya, ganin na
t'saya gardama yasa yace in cire g'yale na da
dank'wali.
Sannan yace lalle-lalle gobe na dawo in ina son
haihuwa, sannan kar nai mishi gardama.
Har muka fito makociya ta da yayarta suna min
fad'an mey yasa na t'saya gardama? Kasa da
kaza,kasance war mun gaji yasa muka sauka
gidan yayar makociya ta.
Muna a gidan zaune sai ga nan y'ar matar ta
farko ta shigo tana masifar kan wai uwar bata
bar musu abinci ba. Yarinya har murguda baki
take, sai uwar taji kunyar gani zaune ta tashi ta
jata waje tana nad'a.
"Wato abinda naji yarinyar na fad'a wa uwar ba
karamin tsorata nai ba, ina k'allon makociyata
itama ta fita tana kumfar bak'in wai ta kara
mata.
Yarinya sai ashar take maka musu ita da uwar
tana Allah ya isanta.
Hakan ne yasa na leka dan ganin shin da uwar
take wannan zagin ko wa?
A inda nake ban mat'sa ba ina mai k'allon yadda
ake dam6e t'sakanin matar nan da y'arta tana
karo mata zagi da Allah ya isa, tuni nai d'aki na
suri jakata na barsu nan,ina jin makociya na kira
na gaba d'aya na rikice.
Tabbas Allah ya soni da har ya nunan wannan
abin da ido na, ba shakka wannan irin yaran su
ne wanda naje nema na kusa 6atar da kaina
wato " Y'AY'AN ALLAH BANI.
Tun daga ranar gani nake na ma Allah butulci,na
ci amanar Miji na dan na tu6e g'yale da dank'wali
gaban wani kato, sai d'ai nasan rashin abokin
shawara na gari ne ya ja min da son zuciya.
Ranar nai kukan nadama har naji ba dad'i, cikin
zafi na d'akko laya nasa mata kalanzir na kona,
sannan na tittilar da turaten yabi shadda.
Sam al'amarin haihuwa nama jingine ta gefe,na
hau istigfari zuwa ga Allah,bisa had'a shi da nai
da wanin shi.
Ana haka Salman ya gama gininshi muka tare,
sai d'ai da kaga gida kasan na zaman mata biyu
ne.
Anan ne na samu makociyar k'warai, mai nuna
min komai nufi ne na Allah, ita kad'ai nake kaiwa
kuka na naji dad'i.
Sam na nisanci kowa, in kinganni a gun dangin
Miji ko gidan k'anin Baban mu toh biki ake koh
suna.
Shima a tsatssaye zan shiga na fito, da wannan
kawai na soma samun sa'ida, sai kuma aka dawo
fad'in dan mijina yai kud'i shi yasa yanzu na fara
dagun kai.
Sai kawai na bisu a hakan. Har na shekara
takwas da aure.
Anan ne nake jin labarin dawowar likita gun
makociya ta, kan yanzu ya karo karatu ana ji
dashi.
Zuwan farko yai mamakin jin har yau ban haihu
ba, hakan ne yasa ya kara rubuta min ''HSG",
sannan ya k'ar6i numbern Salman.
Ran litinin sai naji yace na shirya muje asibiti
yana dan 6ata rai.
Kamar wanchan yauma na wahala gun wankin
cikin, sai d'ai g'wajin da ya fito ne yasa daga
ranar Salman ya d'aina zuwa asibitin, dan likita
ya tabbatar mishi da a gaskiya ba wani "hope",
wai k'allemun mahaifata d'uk sun ru6e,wato
"tubal damage" a gaskiya likita bai sanar ni ga
matsalar ba, amma na tsinkayi wayar Salman shi
da wani abokin shi,
Gaskiya karan nan ban "losing hope" ba,na
sanarwa Umman mu tace nai ta adu'a dan tanaji
ajikinta tabbas za naga dan kaina InshaAlllah
k'wana kusa.
Ana cikin haka Salman ya t'siri abin kirki,tashin
farko mu kaje Umara, muna dawo wa ya fara
koya min mota.
Sosai naji dad'in yadda baya damuwa a rashin
haihuwa ta yanzun, sannan in nace zani asibiti da
kanshi zai kaini ko ya ban mukulli. Kullum abu
d'aya ne in naje,sai likita ya rubuta min awun
fitsari d'uk karshen wata.
Sai ta karasa da d'an murmushi mai kamar kuka.
"Ranar ina zaune parlour ni da makociya ta ina
fad'a mata irin abinda Salman yake min na alkairi
tana murmushi sai gashi ya shigo da murna.
Wai nazo naga abin mamaki, a ranar salman ya
mallaka min mota tawa ta kashin kai. Sosai nai
murna,marar na baki misali, ana nan koh wata
biyu ba ai da yin haka ba naji a gari wai Salman
aure zai yi, har ma an kai sadaki.
Hawaye ta goge wanda ya zu6o mata, kan tai
murmushi, "kawai ni kuma sai na sa mishi ido
naga iya gudun ruwan shi.
A ranar wata laraba sai ga y'an gidan su nan
kusan su biyar wai sunzo ganin d'akin amarya
yadda yake tun kan tazo.
Ina jinsu suna yadda magana wai alkadari na
akan d'an uwansu ya karye tunda gashi da kanshi
ya nemi aure.
A ranar naji takaici, dan Salman ya nunan ni ba
komai bace, abu tun inaji a gari gashi har ya
tabbata.
Ranar kamar kullum nai shiri na nai d'akinshi,
yana a k'wance yana waya.
Yana ganina sai ya fara kiran wai zai kira, zai
kira, tuni na gane da amaryar yake waya.
Sai nai murmushi na zauna a gefen shi, tare da
d'aura kaina a kafadarshi, dak'yar na iya saita
hawaye na basu zubo ba, wai yau har Honey
Salman ke ce min? Dan takaici kawai sai na
zame na k'wanta.
Sai ya mat'so da tambayar koh lafiya? Kai kawai
na K'ada mishi, "kai kad'ai za ka iya bani
mutuncin da kowa zai ga d'auka Salman, kai ne
kawai za ka bada kofar da wani zai k'alleni yace
min ban isa ba... Sai na fara kuka.
Nan ya hau wayan ce wa,kan wallahi kunyar
fad'a min yake, sai nace mey fa? Sam sai na
nuna ban ma san komai ba.
Anan ya sanar ni komai ba ko kunya, kuma wai
saura wata biyu tazo. Kai kawai na k'ada, tare
da mai fatan alkairi.
Sam tunda aka fara rad'a rad'en auren Salman na
ma manta da zuwa asibiti na d'uk wata.
Sai da jiya ta ciwo ni akazo wai za'a kai kayan
amarya gobe ga nawa, harda fad'in fatan su ta
cika musu gida yara.
Sai nai murmushi kawai, a lokacin ne na tuno da
asibiti.
Fure ta k'allo tana goge hawayenta, itama Furen
harda kuka, ashe nata nafila ne akan wasu?
Hannunta Fatima ta ruko, "kinsan mey ya sani
kuka da naga "positive" a result na? Kai Fure ta
k'ada tana mai k'allonta.
Sai ta juya gefe da fuskarta, "wallahi tunda nake
ban ta6a jin kunya ta mahaliccina ba irinta yau,
na sa6a mishi, nai kuka,har nakance Kila wani
lefi nai wa Allah shi yasa bai ban haihuwa. "Nayi
kuka ne saboda Allah ya nunan komai lokaci ne,
gashi kuma na gani, cikin da ban ma san dashi
ba,gashi a zuwa d'aya ya saukar da Ayarshi
akaina.
By
Feenat Ja'afar.
[4/27, 5:31 PM] Feenat Ja'afar.: "JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
32_"Sam na manta da cewa bawai rashin so
bane yasa Allah bai ban haihuwa ba,da So ne,da
na tabbatar ya bawa Nana Aisha(R A), dan Allah
na son d'uk wani abinda Manzon sa ke so, na
kuma sani a d'uk duniya babu Wanda Annabi yafi
So irin Nana Aisha,, tabbas wannan ma Aya ce
da Allah yake son nuna ma dan Adam, amma na
rasa ina "TA'UHIDI" na yaje a lokacin.
"Gashi yanzu na rasa falala biyu a rayuwa, ta
farko hakuri,na biyu mukami, dan nasha jin ana
fad'in cewar ''Allah yana kunyar had'a ido ga
wanda bai bawa haihuwa ba har ya koma gare
shi ranar gobe kiyama.. Nayi imani ba abinda a
duniya Allah zai hana ka ya kuma ji kunyar ka
irin wannan, amma na manta,har sai da ya kure
kan na hango shi, na rasa wannan falalar. Sai ta
fashe da kuka.
A gaskiya yau Fure ta kara samun tuni a game
da rayuwa, har batasan itama ta fara kuka harda
shassheka ba. Chan cikin kuka Fatee tace,"shi
yasa nake son dan Allah ka'r kiyi ma Allah
butulci irin nawa, ki k'ar6i K'ADDARA a d'uk
yadda tazo miki, dan gudun irin wannan rana ta
kunyar Allah.
Kai Fure ta k'ada.
"Idan anyi Duniya dan Manzon Allah daga rana
irinta ta yau bazan kara da na sani akan ban
haihu ba.
"Zan d'au hakuri,na kuma juri jin yadda ake
kirana da JUYA.
"Tabbas yau na gane kuran kuka,sannan na
tsorata da jin labarin D'an Allah banin waccan
matar.
Kai Fatin ta k'ada mata, kan tace.
"Kawai na amince miki ne tafar d'aya a ganin ki,
ubangiji ya baki damar cinye jarabawar ki sister,
kar ki bi yewa mutane, za su kai ki ne kawai su
baro.
"Sannan ki d'aina sanya tunanin kowa a ranki sai
Allah,InshaAllah za kiga d'ai d'ai...
A takaice Furen ta sanarta itama tarihinta,
sannan da address nata, suna cikin haka sai suka
ji dirin mota a kofar gate, sannu a hankali sai ga
nan mata na shigo wa da dangin mijinta su biyu.
A wulakance y'an uwan su Salman d'in suka
k'allo su,ba koh gaisuwa suka cewa dangin
amarya su shiga ga nan "part" d'in amarya.
Da ido Fure tace tai musu magana.
Sai ta d'aure ta gaida su, sosai da ganin su
tasan za'a buga da amaryar.
Har suka gama dak'yar ta kai musu ruwa shima
da sa bak'in Fure.
D'uk dangin amarya sunyi waje,sai dangin
Salman da suka t'saya karewa parlourn Fateen
k'allo suna ta6e baki, ganin ya sauya mata kaya.
Ci kanku bata ce musu ba, sai d'ai sukai kitchen,
d'uk dan su takali fad'a.
Wannan karan kam fatee kasa hakuri tai kitchen
d'in Fure na kira amma sai sa ta karasa.
A bak'in kitchen d'in ta t'saya, bud'e bud'e suke
mata suna fad'in "haka d'ai, sai d'ai a ware ciki
aci aka iya ai kashi, sai ta basu hanya, K'anwar
Salman d'in sai da tazo d'ai d'ai kusanta ta sau
mata t'saki.
Batai wata wata ba ta sharara mata mari, tuni ta
dafe kunci, "ni kika mara? Tass! Ta kara mata
wani, wai sai tazo zata rama, ina, Fati da wa
Allah ya had'a ta, tuni ta hau jibgarta kamar
Allah ya aikota.
Fure da d'ayar K'anwar tashi suna ko'k'arin
bambare Fati, ganin taki dagata yasa tai waje,
sai da ta huce d'uk wani haushi da suka zuba
mata tukun ta bari Fure ta k'waceta tana haki.
"Ihu yarinyar take dan sosai ta bugu gun Fati.
Da gudu Salman ya shigo da K'anwar da dangin
amarya.
Tuni Fati ta sauya kama ta rike k'ugu, wallahi
yau yadda take jinta tai imani ko Salman zata iya
nad'a mai duk'a.
A yadda yaga Fatin tabbas shima ya tsorata, dan
Sam bai ta6a ganin ta burkice haka ba, "Fatima
ya haka fisabilillahi? Abinda ba halinki ba shine
yanzu zaki t'sira saboda zan kara aure? Wannan
ai hauka ce.. Wata uwar harara ta sau mishi, kan
ta k'allo k'annen yadda suke doka mata harara,
data zabura tace "ku t'saya,ba akan ku na
haukace ba? Sai tai kitchen,''yau wallahi za kaga
d'anyen kai.
Bai nufa yaga ta fito da gudu da muciya tai kan
k'annen shi da dangin amarya, habawa,takai ta
kai, kowa hanyar gudu yake nema, har gate ta
bisu tana muka musu a d'uk inda hannunta ya
kai.
Fad'i take "ba haukatar ni kuke so kuyi ba? Bari
toh na fara ta kanku, haki take tana "naga wata
shegiyar da zata kara zuwa har gidana ta ci
mutunci na d'an... Saukar Mari taji a fuska, da
sauri ta y'ar da muciyar ta K'alloshi tare da dafe
kunci.
"Salman... Mari? Ni ka Mara? Cikin tunzura
yace"an mare ki d'in.. Koh nima zaki dake nin?
Kai ta girgiza,tai cikin parlourn, kawai sai ya bita
yana kara sauke mata sababi,
"Aure ba fashi, wallahi sai d'ai kiyi abinda zakiyi,
dama tunda naga har yau baki tanka a auran nan
ba nasan da abinda kike shirya wa.
Da mamaki take K'allonshi.. Kan ta rint'se ido da
murmushi ta furta "Na Miji?Namiji? Kawai sai tai
k'wafa.
" Ba laifinka bane, sai d'ai ka sani, wallahi na
bazan zauna na jidi wannan rainin hankalin ba
har wata ma ta shigo ta kawo min raini ba..
Hannu ya hard'e kan ya k'allota, "yanzu mey kike
so ayi? Da sauri tace "saki.. Kai Fure ta hau
girgiza mata, sai ya k'allo Furen yai
Murmushi, "toh wallahi bazan saka ba,aure kuma
kamar anyi an gama ne.. Cike da bala'i tai woo
kanshi, "wannan ne kuma baka isa ba wallahi.
kawai sai ta rufo kofar parlourn,"in har ka fita a
gidan nan toh ka Sake ni, na tsane ka, ban son
ka, koh kaunar ganinka yanzu bana yi.
Kafada ya make, "kiyi komai amma wallahi bazan
sake ki ba, sai d'ai zaki iya zuwa ko'ina ne in ma
baki son ganin zuwan amarya bazan hanaki ba. A
masife ta ta kutuntumawa Amaryar zagi, kawai
sai ya hau mata dariya.
Ganin tana neman fita a haiyacinta yasa Fure
kamo ta. Sai sukai d'aki. Tuni ta hau tattare
kaya. "A'a sis Fatee, jama'a za su miki k'allon
kishiya ce ta kore ki fa... A masife tace"sumin..
In dai jama'a ne ai ko na zauna zasui komai,
wallahi bazanyi kaffara ba sai na bar gidan nan.
Yin duniya Fatee taki hakura.
Sai da tai katuwar "trolley" kan ta janyo taiyo
parlour kan ta koma d'akko hijab,, yana ganinta
ya mike, dan sam bai zaci da gaske take ba.
"Fatee kar muyi haka dake, a masife ta ja jakar
har tana bi da ita ta kan kafarshi, har ta kusa
kofa ta tuno da jakarta, ita d'ai Fure sai binta
take a baya tana tai hakuri.
Jakarta ta zuge, cikin masifa take birkito kayan
ciki, "ga Fatee matsiyaciya, "cheque" dinshi ta
hulla mishi, kan ta d'au mukullun mota, "duk ka
jika kasha, ni ba masiyaciya bace, sannan ka
sanarwa da dangin ka su zuba ruwa a kasa su
sha, na barka har abada.. "And 2 hell with
amaryar ma.
Ganin gaske ta d'au zafi yasa kuma ya kid'ime,
"Fati ka'r kuskura ki fita ba da izini na ba,
Fateema, ko ta kanshi bata bi ba, burin ta kawai
ta bar gidan, mukullin Fure ta k'ar6a ta bud'e
mota, a baya ta sa jakar, sai gashi ya fito, "Fatee
ki saurare ni pls? Yanayi yana k'allon Fure kamar
mey nufin ta sa baki, ita kam Fateen ma sai ta
fara bata tsoro,don d'uk ta firgice mishi.
Shiga tai da zummar tada motar ya rike kofar
gam, "Fatima pls, kira take "ka cikan murfi mota,
ba kace naje ko'ina ba? Kai ya girgiza, "hakuri,
wallahi da wasa nake.. A tunzure tace "wasa? Da
sauri ya jijjiga kai, "eh, kiyi hakuri.. Wallahi ko na
kira su Abba? Da tai wani kukan kura da k'arfi
taja murfin motar, "Allah baka sa'a.
"Reverse" ta fara yana kiran sunanta, amma ina,
ga unguwa kamar ta mayu ba kowa layin, da
sauri ya shiga dan d'akko waya yasan Abba
kad'ai zai t'sayar mishi da Fatima.
By
Feenat Ja'afar.
庐NWA
9/29/16, 2:39 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 33_Sosai take kudu
dan ma kar ya cimmasu tai ta k'wane-k'wane,
sai da ta tabbatar da ta mishi nisa kan tai
"parking" achan gefen titi tana k'allon gabanta ba
koh kiftawa, haki take tana jawo numfashi
tamkar da kafa tai gudun. Fure ta k'allo ta "Kiyi
hakuri ki kori shedan sis Fatee... A "stirring"
motar ta d'aura kanta ta sau wani kuka mai
k'arfi, kawai sai Furen ta zuba mata ido dan ko
zata huce ta hakan. Sosai tai tana mai kara
t'sanar halin mutum. Sai da tai mai isarta kan ta
share, a sannan Fure ta fara ce mata komai yai
zafi maganinshi Allah, ta duba halin da take ciki
kar ta jama kanta matsala. Ita d'ai uffan bata ce
ba,sai ma hawaye dake k'waranya. Wayan ta taji
yana kida, a hankali ta sa hannu a jakar ta ciro,
"Abba" ta gani, tuni sai ta seta kanta kan ta
d'auka. Ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba,
sannan ya sanar mata kar ta fara dosar inda
suke tunda akan kishiya zata sa6i mijinta. Har ya
kashe in banda kuka ba abin da take, sai ta
share idon, kawai sai ta raya mata tai yola
dangin Ummanta kawai, Fure ta k'alla sai tace
tazo ta tuka. Ba musu sukai musanye, "kaini
tasha.. Kai ta k'ada mata ba musu, sai ta d'aura
kai a gefen kujera tana k'allon gefe hawaye na
t'silalowa. Kai ta daga ta k'alli Fure lokacin da
taji tana "Horn" sai Furen ta d'auke kai. Har suka
shiga gida bata k'allo ta ba. "Tasha nace ki kaini
fa.. Fita Furen tai had'e da bud'e baya ta ciro
kayan Fateen. Kawai sai ta bita taga iya gudun
ruwanta. A parlour ta sauke, a takaice ta karewa
ko'ina k'allo kan ta zauna, sai Furen taje "fridge"
ta d'akko mata sassanya ta tsiyaya a cup tare da
tsayawa a kanta ta bata. D'uk sai kuma ta fara
kunyar Furen,ba musu ta k'ar6a tak'wa shanye
tare da mikawa Fure,kara mata tai kan ta zauna,
tuni sai ta sau ajiyar zuciya. Kai shedan mugune,
nan da nan zai sa ka tafka tsiya zuwa anjima ka
dawo kamar ba kai kai ba. "Koh kud'in mota baki
taho dashi ba,hala zasu kai ki k'yauta? Sai a
sannan ta tuna da ba ko sisi d'uk ta zube mishi
t'siyarshi. Yanzu mui sallah,sai muci abinci,"I
know babyn mu yau ya jigata, dan yau Momyn
shi taji k'arfi... Dariya suka sa Fateen na goge
hawaye. Sallah sukai ta d'akko mata dan
"snacks" ta rage kan ta tafasa musu ko taliya ne.
Zama tai lokacin da take dumama miya tana
murmushi, "Ashe kin iya fad'a haka sis? Kai koni
na tsorata fa, kai ta k'ada. "Mutane ke koya
maka d'uk wani hali da ba naka ba. "Amma
wallahi da gaske na t'sani Salman, ko ganinshi
na t'sani yi, sam namiji bai da tabbas. Kai Furen
ta k'ada, "kiyi hakuri, komai mai wuce wa ne. Ki
zauna anan zuwa gobe AA ya dawo sai ya bamu
shawarar yi.. Da sauri ta k'allota, "namiji ne zai
bamu shawara? Da rashin fahimta Fure ta k'ada
kai, sai ta girgiza kai,"toh a gaskiya bazan zauna
ba, dan maza sun shani tuni na warke... Kiran
Salman ne ya shigo tana ji taki d'auka, dan "ring
tune'' nashi "special" ne. t'saki ta ja ta tashi ta
d'au wayar ta d'anna "reject" kamar ta cire
"buttun" d'in wayar. Ko ajiye ta batai ba ya kara
kira. Kawai sai ta kashe wayar gaba d'aya.
Shikam suna fita ya dawo d'aukar mukulli ya kira
Abban Fateen, suna gamawa sai ga nan kiran
likita, da mamakin shi ya ji yana mishi "congrats"
wai ya zama Baba.. Kamewa yai gu d'aya lokacin
da yace ma likita shi bai fahimta ba ya sanar shi.
Sai ga nan takardar asibitin ya d'auka da ta bari.
Kai ya dafe kai, har da k'wallarshi, wanda bai san
ta meye ba. Abu d'aya ya sani yaso Fatee har
yau d'in nan. Tuni ya bisu ko zai same su, shine
har tasha amma ba Fatee ba kalarta. Dak'yar
Fure ta shawo kanta ta zauna suka k'wana,
kusan k'wanan zaune sukai suna firar duniya, fir
taki ma k'unna waya bare a kira ta. Washegari
Fure da taryar AA ta tashi, sai d'ai Fatee na
tayata tana ta6e baki, dan gaba d'aya maza sun
sane mata t'saf. Ita dai Fure murmushi kawai
take binta da shi. By Feenat Ja'afar.
Like 路 Reply 路 Report 路 Apr 28
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 34_Sai kusan magriba
AA ya shigo, a gajiye yake, lokacin suna a d'akin
baki ita da Fatee kan lalle ita sai ta tafi, suna
cikin gardamar taji dirin motar shi, sai ta fita tare
da kulle Fatee ta waje, sam bata so ta tafka
kuskure. Kamar ba kowa ta t'ar6e shi da fara'ar
ta, kamar kullum ya kimtsa kan yaci abinci, sai
kawai suka hau soyewar su ta ma manta da
Fatee. A zabure ta mike a cinyar shi a parlourn
tai d'akin baki da gudu, da sauri shima ya mike
yana "lafiya pretty? Tana bud'e ta tana zaune a
gefen gado ta k'wando mata harara. Sai ta kara
rufota kan ta kama hannun AAn sukai d'aki. A
nutse ta sanar shi komai harda hawayenta, sai
kai yake jinjina wa, lalle taga tasku, amma yafi
ganin lefin mijin. Parlour suka dawo ta kara bud'e
Fatee, kamar mey jira sai gata sanye da g'yale
da Jaka a hannu, "dan Allah karki t'sayarni, ki
barni na tafi nagode k'warai... Shiru tai ganin
Ahmad, sai yai mata k'warjini har batasan ta
gaida shi ba, hakuri ya fara bata kan tai hakuri
yanzu magriba tayi, zuwa gobe sai su san abin
yi, ba dan ta so ba ta hakura,kawai sai taga
girman shi. Ita kanta Fure ganin AAn sai taji tana
d'an dari dari dashi, dan kawai d'aurewa take,
amma ace gaba haka ya faru da ita wai... Hmm
sai Allah kawai. Fitowarshi a wanka kenan yaga
ta had'a tagumi, sai ya k'ada kai, tabbas yasan
maganar dazun ce. Yana k'allonta har ya gama
shiryawa ta lula duniyar tunanin dabi'ar maza da
mutanen duniya. Sai ya k'ada kai,a hankali ya
tako ya iso gabanta ya tsuguna. Ajiyar zuciya ta
saukar,kan ta d'an k'ak'alo murmushi, sai ya dafa
cinyarta, "I love you pretty... En banson ki sanya
shakku, ki cire tunanin komai a ranki, AAA naki
ne... bazai ta6a miki haka ba InshaAllah..
Hawaye ne ke ko'k'arin zubo mata, so take ta
gaskata shin gaske AAA nata ne? Sai kawai ta
sau su suka zubo, hannunta ya ruko,har yanzun
yana a tsugune, "Furii believe me, maza ba d'aya
ne ba... Tuni ya hau tsumata da dad'in
baki,Aiya,ita kam ta ziru t'saf, sai yasa hannu ya
sunkuyo da kanta da take murmushi hawaye na
k'waranya yasa ''lips" nashi yana tarar su. A
hankali ya dago ta suna k'allon cikin idon Juna,
tabbas ta aminta AAA na daban ne a sauran
maza, a hankali ta zamo itama tai yadda yayin
suna mai cigaba da karantar juna ta cikin ido, sai
ya tadasu t'saye tare da lafar da kanta a gun
zuciyar shi, a hankali tamkar wata baby yake dan
jujjuyawa kad'an kamar mai rawa,ita kam Fure
anyi luf..cikin nutsuwa ya kara karasa ta da
wakar da indai yai mata take jin a sama. Takanji
wani nishad'i, har ta manta da komai, sam in kaji
yana wakar ka zata shine mawakin, amma kawai
dan Furen shi baitin na "Nothing gonna change
my love 4 you.... Yake burge shi. T'saf acikin
daren ya ware Prettyn shi cikin sauki da lumana,
har ya lalla6ata tai bacci fuskarta d'auke da
murmushin son shi da jin dad'in baitikan, da yaso
yin shiru, sai ya ji tana ya cigaba. Murmushi yai,
Mata sai da lalla6a. Da safe suna kitchen yana
tayata had'a ''break" ta fito da dan gudunta, a
zaton ta ita kad'ai ce a kitchen, hannunta ta cire
a wuyan AAn taiyo gun Fateen da ta juya. "Sis
lafiya? Gaskiya a d'aina gudu da d'an mu.. kawai
sai taji ta ruko hannunta da murna ta d'aura kan
cikinta, "wallahi yau sai mot'si yake, cikin murna
Furen ta kara d'aura d'ayan hannun tana
murmushi, Allah sarki Fatee, fara'a take kamar
mey, shi d'ai Ahmad daga bak'in kofa yana ta
musu murmushi. Sai lokacin Fatee ta kula dashi,
a dan kunya ce ta gaida shi, sai ya amsa yana
ya Baby? Sai tai kasa da kai shi kuma ya shire
"apron" nashi yai waje. Kitchen d'in suka wuce
dan gama aiki, sai g'yada kai Fatee keyi ganin
yadda Fure ta zama "Chief ". Bayan sun gama
cin abinci ya shirya yace Fure ta kira Fateen. Sai
gasu sun fito sanye da Hijab. Sanarta yai ya ji
komai, sannan ta zauna anan zuwa yai ma su
Abban ta magana, ya d'ai lalla6a ta har ta yarda.
Cikin wayo yasa Fure tai mai "copying" numbern
mijin Fateen. Sosai take jin dad'in zama da ita
kamar sun saba a k'wana biyu. Iyanzu kam,ji take
Fure tamkar y'ar uwa ce a gunta. Cikin dabara
Fure tasa ta bud'e waya kan zasui "exchanging"
number. Tana bud'ewa "texts" d'in Salman na
shigowa, d'uk na ban hakuri ne zuwa wai ina
take? Tai mishi rai ta dawo, tabbas itace ma
had'in rayuwar shi, baki ta ta6e, "yau na gama
yarda da dad'in bak'in maza... Ji ni zai rai nawa
hankali? Wai mahad'in rayuwar shi? Fure tai
murmushi, kawai sai tai k'wafa ta hau goge su
tana mita. Ita d'ai Fure dariya take tana tai
hakuri. Shikam yana d'akin Fatee ya tasa "result"
yana k'allo, waya ake mishi kan yau za'a zo jeren
amarya, sai yai jim, "ba yau ba. Kawai sai ya
kashe waya. "Delivery report" ne ya fara shigo
mishi, da halamu kenan Fatee ta bud'e waya. Da
sauri ya fara dailing, da kamar bazata ta d'auka
ba, sai d'ai ta waske, ''ya akai? Cikin magiya ya
fara "Fatee, Fatima,Batool, haba Bintu na, dan
Allah ina kike? Kiyi hakuri pls... T'saki tai, "kaga
fa, ni wallahi wannan mayaudaran kalaman naka
bazasu min kom ba, ka ma d'aina tambayar ina
nake, dan wallahi bazan fad'a ba. " Haba
Batula,gaba d'aya kinsa na fita hayaci na, auren
ma d'uk ya ficen a ka, ga nan Umma ta tadan
nata akanki itama... Da sauri tace "kar ka maida
ni bi ta chan, ka zata fasa auren ka zai damen
ne?.. Kawai sai taja t'saki ta kashe. Fure tace "a
gaskiya yayi nadama fa man d'in nan.. Harara ta
dan sau mata, "ke fa na fuskanci bakisan halin
maza bane. Kai ta k'ada tana murmushi, sai ta
ajiye waya zata kama ruwa, tuni Fure ta sace
numbern Salman. Da yamma suna zaune suna
wainar filawa sai santi Fatee take, wani abu na
ciki, tunda taga positive Washegari ta t'siri
t'surfa. Fure sai dariya take mata, "haba mom
twins, Wa'ina ai sai Kano, kai ta g'yada tana
d'ang'walar y'aji, "haka ne kam, amma ke komai
naki ai "special" ne... T'sam Fure ta zuba mata
ido tana k'allon ta, ita kam sai zuba santi take,
"yajin ki ma na daban ne, a k'wana uku na koyi
abubuwa... "Lafiya wannan k'allo? Kai ta k'ada,
dan har ta Lula duniyar tunanin AAAn ta,tunda
tace koman ki "special" kawai shi ta tuno. By
Feenat Ja'afar.
Like 路 Reply 路 Report 路 Apr 28
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 35_Bud'e gate suka ji,
Fatee tace "d'an mikon g'yale na, hannu ta mika
kan ta yafa mata. Shi kad'ai ya shigo yana
murmushi, kai kasa Fatee tai mai sannu da
zuwa. Sai ya nuna wa Fure waje da hannu, kan
ya dawo kanshi,yana nufin ta d'akko mayafi, kai
ta g'yada, sai yai waje, ta d'akko ta tarar Fatee
zata shiga d'aki, tace "A'a. Mui zaman mu, zasu
zauna taji Ahmad na fad'in"bissmillah man, shigo
daga ciki. Juyawa Fatiman tai zata tafi d'aki, a
tunanin ta ko bako yayi, sai ta ji yace "bissmillah
Fatima, dawo kiyi zaman ki, tana juyo wa tai
ar'ba da Ango. Tuni ta k'ank'ance ido tare da rike
k'ugu, sai ya marairaice mata, kawai sai yaga ta
kara mishi ma k'yau dafari. "Mey ya kawo ka?..
Cikin marairaita ya matso, ''haba Fati ta, kamshin
masoyi ai baya buya koh AAA? Sudai dariya suke
musu. Harara ta sakar mishi, "kar ka yaudari
k'anka, dan ka d'auka ban sanka ba All... Shiru
tai ganin ya zube mata g'wiwa biyu a gabanta.
Sai ta k'allo su Fure, itama k'unne ta kama kan
tai hakuri. Sai ta d'auke kai, "tashi malam,bani
da matsayin nan, tashi, maza ka rufan asiri..
Ahmad ya k'allo, sai yai mishi da ido kan ya
cigaba da gashi. "A'a Batool, wallahi kin girmi
hakan, kinsan fa ina kaunar ki, believe me... Sai
yasa hannu a wuya halamar ya rant'se, tuni sai
ta fara hawaye, da zummar samun nasara ya
kara k'allon Ahmad, da halamun d'ai shi ya kit'sa
mishi komai. Sai Fure ta k'alleshi da tuhuma tana
k'anne ido d'aya, da sauri ya daga kafada
halamar ba ruwan shi. "A'a, g'wara ka auro mai
haihuwa,, kaga k'wanka kaima a duniya koh? Ni
kuma banni rai.. Kawai sai ta fashe da kuka. Da
sauri ya matso ta kara ja da baya.. " A'a Fatee,
gashi ai Allah ya bamu, kiyi hakuri nayi kuskure..
Sai ya k'allo Ahmad da ke girgiza kai halamar ya
k'wafsa, bai aune ba ya ji ta doko kofar. Bugo ya
fara akan ta bud'e dan Allah, tana kuka tace dan
ciki yazo ba dan ita ba, kuma ciki nata ne ya tafi
kawai. Yin duniya taki bud'ewa. Dak'yar yabar
gun Ahmad ya jashi suka fita, "gaskiya kai su6ul
d baka, sai da nace kar ka nuna mata kasan da
cikin nan, za ta d'auka shi ya kawo ka. Kai ya
dafe, "toh ya zanyi? Wallahi ni Fatiman ce d'uk
ta ban tsoro,sam bamu ta6a haka da ita ba.
Dak'yar yace ya dawo gobe kan sun shawo mishi
kanta. Sai bayan isha'i ta bud'e dan yunwar
cikinta. Fure na parlour, harara ta sau wa Furen,
kan ta zauna, "yi hakuri, ga nan abincin ki kici,
k'allota tai, "baga nan irin halin mazan da nake
fad'a ba, sarakan san kan tsiya, Allah ya kaimu
gobe da safe ku ga. Ita dai Fure murmushi kawai
take. Washegari bak'wai da rabi a gidan ta mishi,
Ahmad ya dawo a jogging ya tarar da mutum a
kofa. Sai ya jinjina kai,lalle Fatee ta kunno wuta.
Matar da ta gama shirin tafiya sai gata ta bingire
da bacci,har d'akin Ahmad yace ya bita, ganan
jaka ta had'a tai "ready". Gadon yaje ya zauna a
kusan ta cikin sand'a, tana t'saka da bacci taji
ana kamar shafa mata mara, da sauri ta bud'e
ido, tana ganin shi ta sau kara tun k'arfinta, da
sauri yasa hannu ya rufe mata baki,batai wata
wata ba ta gant'sara mishi cizon da ba shiri ya
cire hannun, "waya baka izinin shiga d'akin
jama'a? Cikin jin zafin hannu yace "ban sani ba
d'in,, kofa ta nuna, "toh fita, matsowa ya fara,
"ba inda zan fita fa, mai gidan yace in shiga.
Ganin yana kara matsowa yasa ta fara duben
abin duka,kasa ta s'akko da filo a hannu,"kar ka
matso nan, tsayawa yai, kan ya kara zubewa,
"toh kiyi hakuri, wallahi na tuba, harara ta sakar
mishi, "kai kasan wannan, ganin ta ki da lumana
shima ya fara fad'a, "dole ki koma, a tunzure tai
parlour tana "toh sai naga dolen, kawai sai yaja
mata jakar chan, "haba Fati.. Ganin su Ahmad
yasa yai shiru, "Dan Allah ku bata hakuri.
"Fatima kiyi hakuri, d'uk dan Adam yana da
hakan, amma ki duba yai nadama, Fure ta k'allo
wace ke magiya,"bai ba wallahi, Ahmad
yace"yayi man Fati, kawai sai ta sa musu
kuka,nan suka had'u suna bata hakuri,komai
sukace Salman sai yai kalar tausayi yace ''na
daina. Sai ga Fatee ta fara kukan shag'wa6a, su
Fure sukai d'aki suna leken su, tun in ya mat'so
tana ture shi har ya runkomota t'sam, sai kuma
yace mata yunwa yake ji, kai suka k'ada, "lalle
Fatee matsala, cewar Ahmad. K'allonshi Fure tai,
sai suka rufe d'aki suna dariya. A ranar suka
d'inke t'saf da Salman d'inta. Da zasu tafi suka
shige d'aki da Fure, dariya take mata kan ta
g'wara bawan Allah, "Hmm,bazaki gane ba, ni
nasan mey nasha a baya ai, sai d'ai wallahi har
na haihu ba mai gani na a dangin shi, amarya
yasan inda zai kaita ba a gida na ba. "Na haihu
kuwa, in kika cire Umma.. Toh ba d'an uban da
zai d'au d'ana wallahi, dariya Fure take, "a
assasauta d'ai, tace "za ki gani ai.
************************ Sadakin Maryam aka kai,
d'uk Wa'inar nan da ake toyawa sam Hassana
bata ji ba. Anan yayan su Ahmad ya fallasa
Momy taji wai K'anwar Fure aka kaiwa, nan ta
tada tsiya. Kan wallahi in dai za'a auro Maryam
toh Sai an auro Rukayya. Takanas Momy ta
Wanki K'afa har gidan Fure ta kare mata tass!
Wato wai so take ta gaje musu dangi da t'siya?
Toh tasan da saninta, indai har ta yarda auren
Muh'd ya faru da Maryam, toh wallahi itama
Rukayya sai ta shigo mata.. Da sauri Fure ta
rint'se ido hawaye ya zubo. Tab,ana wata ga
wata. Tunda har Momy ta rant'se toh k'wa tasan
Rukayya ta shigo ta gama... Hannu ta d'aura aka
hawaye na zubar mata, a hankali ta furta "wayyo
ni.. tama kasa koda ihu ne taji dad'i,kukan ma
sai hawaye, koh wata biyu ba ai da kashe "case"
d'in Fatee ba ga nata ya d'anno. By Feenat
Ja'afar. 庐NWA Feenat.mywapblog.co
9/29/16, 2:41 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
36_Tamkar mara lafiya haka tai lamo akan
kujera,har maigidan ya dawo, sam shima bai
shigo da walwala ba, sai d'ai yana ganin Furiin ya
rikice mata. Dan yanzun daga gidan yake Momy
ta sanar shi tazo, ga yaje gun Abba,Abba yace
tunda an nace abu kusan shekara nawa kawai ya
hakura ya aure tan, dama bai bi takan mama ba,
dan t'saf yasan abinda Momy tai agun ta ido ne.
"Pretty... Ido kawai ta zuba mishi, sai ya dago
ta,d'uk ta sau mishi jiki k'allo ne nata, tuni sai ya
tsorata, da k'arfi ya jijjiga kafad'unta "Furera... A
firgice ta k'alloshi,cikin sanyi tace "uhmm.. Suna
had'a ido ta barke mishi da kuka.
Juyin duniya Fure taki d'aina kuka, kawai sai ya
sa mata ido shima kamar zai sau kukan.
Jijjiga kafad'unta kawai yake halamar rarrashi
yana share mata hawayen,sai d'ai yana goge wa
wasu na zubowa, kawai sai ya d'auke ta tuni ta
damke ido tana cigaba yai d'akinshi da ita,
"bathroom" ya shiga,ya cika "bathtub" da ruwa,
sai ya bar kofar a bud'e, tana t'saka da kuka ta
jita cikin ruwa.
Da azama ta bud'e idon,ya k'ada yai jajjajir tana
k'allon shi, tuni shima ya fara ko'k'arin shiga ciki,
kawai sai ta kara jiniya tana dan bubbuga ruwan
da shura K'afa.
Shiru kake ji Fure, kuka ya kare. Shi kad'ai yasan
"week points" na prettyn shi, dan ka burkita mishi
ita da kanshi zai samo kanta, gashi yanzu harda
waka kamar ba ita ce dazun ba.
Shi kam yana a bak'in gado yana k'allon yadda ta
zubo da gashi ta gaba tana gogewa da "towel"
daure da wani, tare da wakar "mayafi na bargo
nah.. Sai murmushi yake.
Da hannu tasa tai baya da gashin fuskarta ta
baiyana,mutumin kawai ya zuba mata na mujiya.
"Towel" d'in ta hulla mishi a fuska, tuni ya shaki
kamshin "shampoon" jikin na "vatika" yana
lumshe ido,cire wa yai da zummar hulla mata ta
kawar da kai tana murmushi.
Bata aune ba taji ya janyo ta gaba d'aya suka
suka zube suna dariya.
"Wallahi ki tada musu hauka na fad'a miki, tuni
zance zaisha ban-ban, cewar Fatee da suke
waya.
"Hmm, sis Fatee bazan iya ba, in fa wani yaci
riba,wallahi wani duka zai ci, kar ki manta a
gidan su fa take? Babbar riba ta yanzu na samu
Maryam ta shiga gidan Hassana, wallahi ko
Rukayya tazo naci riba.
"Bari banja da ikon Allah ba, amma in dai kece
Furera Muh'd, Matar Ahmad AAA, wallahi
Rukayya sai d'ai gani da ido t'sakaninta da Mijin
ki.
Ki rubuta ki ajiye, bana ke zakiyi "wining" a
wannan "battle" d'in, InshaAllah daga wannan
karan kin zamarwa Momy ciwan ido,kin zama
k'arfen K'afa, InshaAllah ke da AAAn ki
TAKALMIN KAZA ne.
Ajiyar zuciya tai, sam ta ma sa a ranta Rukayya
fa ita ta shigo ta gama, amma bata isa ja da Sis
Fatima ba, yanzu sai ta hau mata.
"Amin toh, yanzu ma haka ina gida gun shirye-
shiryen bikin Maryam d'in, Fatee tace "ita
Maryam taji zancen? Kai ta k'ada mata, "mutum
d'aya yasan auren Maryam shine fansar zuwan
Kishiya ta ba...
"Sis wallahi ji nake kamar zuciya zata fashe in na
tuno AAA za'a d'aura mishi aure da RUKAYYA.
"Ina matukar son Mijina, shima yana sona, ance
ba'a "BA'A YABON DAN KUTURU" wai sai ya
girma da yat'sa.. "Believe me.. Na aminta da AA,
dan shi ya so ni a yadda nake, gashi yanzu ya
fiddo ni cikin jama'a.
"Sis Teema ya zanyi na rage kishi pls... Buh ki
d'aina k'wantar mun da hankalin kishiya bazata
zo ba, ki barni na zama "ready'' dan t'ar6ar ta.
Shiru Fateen tai, wallahi bata tara sani ga Allah
ba, amma a jikinta take jin tabbas auren nan ba
mai yuwa bane.
Sai dai ya ta iya, kawai sai ta hau lallashinta kan
tai hakuri tai ta adu'a in da alkairi toh.
Kamar Yarinya haka ta sau kuka a d'akin su
Maryam lokacin da suka kare wayar.
Hawaye Maryam ta goge, wacce tazo d'aki d'an
nuna wa Furen gadon da su Ada suka za6a
achan t'sakar gida.
Ba koh sallama ta shiga d'akin, da sauri Furen ta
hau goge hawayenta.
Zama tai tana k'allon fuskarta, sai Furen tai kasa
da kai kamar marar gaskiya.
"Ya Furera kishiya za'a miki amma ba wanda ya
sani? Kai ta dago tana k'ada mata, "toh mey
yasa zaki zabi ki muzgunawa kanki dan kawai jin
dad'in kanki da nawa? Kai Furen tai kasa dashi,
kawai sai Maryam d'in ta tashi tai waje, sai ta
d'aura bayanta.
"Umma! Umma!!.. Cikin shesshekar kuka take
k'wala mata kira, tana zuwa ta wat'sar da hoton
gadon kasa, d'ai-d'ai Fure ta taho,
"Lafiyar ki kuke kuka?
Kawai sai Maryam d'in ta k'ada kai da takaici,
"ku zama sheda toh Umma, na fasa auren nan
wall... Da sauri Fure ta rufe mata baki tana
girgiza kai.
Ture hannun tayi tana hararar Furen, "bari kiji
Fure, wallahi nafi k'arfin ai "playing" wannan
"game" d'in dani daga ke har har dangin Muh'd
d'in..
Fad'i take ita kam sam bazata d'au wannan ba,
tun wuri yazo ya debi sadakin shi ya ware, ita
za'a rai nawa hankali?
"Mai suka maida ki? Sakaryar da baki san abinda
kike ba ko mai?
da har za'a fanshi aure na da kishiyar ki? Kai ta
k'ada tare da rike k'ugu.
Da taga suna bata hakuri ma tai waje, ba ita ta
dawo ba sai da taji kiran Muh'd yana sanarta
yazo.
Ba jima wa ta karaso, wankin babban bargo ta
rufe ido tai mishi, sannan ta jaddada mishi ba ita
ba auren shi, dan sunfi k'arfin cin zarafi.
Gaba d'aya yai mutuwar t'saye jin masifar
Maryam, har ta shige gida kamin ya farga fara
t'sayarta.
Wasa-wasa d'ai Maryam ko waya ta d'aina amsa
nashi, ga a gidan kullum kuka, barin ma da taji
irin cin kashin da dangin ke ma Fure, mamakinta
d'aya "wai shin ina masifar Fure tayi? Ina
wayonta?
D'uk da tana matukar son Muh'd amma mutuncin
y'an gidan su yafi k'arfin komai a gunta.
Sai d'ai shi Abba yace sam bai san zance ba,
tunda taki fad'a mishi dalilinta na fasa auren
k'anin mijin Fure.
Tanan kawai suka samu cikas.
Biki saura sati uku, in kaga Fure d'uk zabge,
amma k'arfin halinta yasa sai mai kula zai gane.
Yauma tana gida, Umma sai tausarta take kan ta
cire damuwa, tabar wa Allah komai, Maryam ta
k'alla wace tun ranar ta d'auke mata kai, sai tai
murmushi.
"Maryam.. Banza ta mata, d'uk da tabar abinda
take. Bata damu ba ta kara cewa
"Maryam tun ranar chan naso son kisan k'in
auren ki da Muh'd tamkar kin bawa Momy damar
cin galabar mu ne, dan dama so take a fasa naki,
wanda nai imani baza'a a fasa na Ahmad.
"Maryam.. Kiyi hakuri kibi zuciyar ki, ni ki bar
nawa gurin Allah, ki sani fasa auren ki, bazai
sauya zani gun Momy ba. Matsowa tai ta dafa
hannunta,d'uk Umma na k'allon su.
"Maryam, kai ta dago tana hawaye, sai ta share
mata.
"Ki min alkawarin sauke gammon nak'in nan da
kika d'aura, ki duba so,da kuma kaunar da bawan
Allah nan yake miki, da naso auren ramako dake,
ashe kana taka Allah na tashi, kar ki bawa Abba
kunya, ki manta dani, ki fuskanci Moh'd, ina
rokon ki...
Dago wa tai ta k'alli Umma, sai Umman ta tashi
ta basu gu, sai ta jijjiga wa Furen kai.
"InshaAllah, amma fa ki sani, wallahi d'uk dan
uban ni da ya nemi takani zan murje mutum.. Kai
ta k'ada mata, "wannan ban hanaki ba, ba kuma
zan fara hanaki ba.
Da wannan ta samu suka d'inke da Muh'd d'in,
aka cigaba da hidimar biki a gidan guda biyu.
Dan sam ko kusa Ahmad bai ko mot'si, asalima
Fure ke tambayar shi wataran kan abinda yake
shirya wa, banza yake mata.
Ita kam bangaren Momy koh a jikin su, d'an ko
ita ta isa yiwa Rukayya lefe, yayinda a bangaren
Mama tasa wa kowa ido, daga Ahmad d'in har
Muh'd,dan ba mai ne manta cikin harkar kara
auren shi.
Ku tambayen ina labarin Hassana man?..Lol.
Hassana d'ai sai ana saura sati wata d'aya biki
kan taji labari, akanzo har gida ana tambayar ta
da gaske mijinta wai zai aure?
Wataran harda shewa zata bada amsar A'a,
Yayanshi ne zai kara aure dan matar ba ta
haihuwa.
A ranar Momy ce ta tare ta da zancen ba koh
rufi, haka ta dawo gida ta hauka cewa Muh'd,
yayi lallabin duniya taki, a fafur sai ya fasa, sai
d'ai a ranar da tasan wa zai auro mata tattare ta
bar gidan.
Sai dawo wa yai yaga gida a bud'e tayi gidan su,
hakan ya bashi damar cigaba da shirin auren shi
cikin nutsuwa da aminci, bai ma kara bi takanta
ba.
************************
Ana saura k'wana d'aya aure har gida Momy tazo
ta chake shi harda kukanta kan wai ya mayarta
mahaukaciya, ita kad'ai take kid'anta a auren.
Tuni yai shiru, Fure dake kitchen d'akko ruwa
tana jin yana fad'in "nifa Momy kar a kaini bango
nai ba d'ai d'ai ba, dan wallahi bazan auri
Rukayya b... Mari ta sauke mishi, tuni Fure da
akai akan idonta tasau "tambulan" din lemon ya
fashe tana k'allon Momy.
Haka ta taka ta durkushe gaban Momyn da
g'wiwa biyu wacce ke kukan dan ba ita wai ta
haife shi ba, amma ai wai ita taci kashinshi har
ya zama mutum
"dan Allah Momy kiyi hakuri, dole zai bi umarnin
ki, zai auri Rukayya, dole ne wannan.
Tun fitar Momy ya kasa ko mot'si daga inda
yake, cikin d'auriya Furen ta fara lallashin shi da
kalamai masu sanyaya rai, kan Momy kam Mama
ce, dole yabi umarninta, kodan ta fita zargin ba
sa hannunta a kin aurenshi ba, dan Allah, kuma
domin ta... Har kuka tai mishi, shi d'ai kala bai
ce ba.
A t'saye yake gaban madubi kamar kullum tana
shirya shi, sai d'ai yau shirin na daban ne, dan
wai shirin d'aurin auren kishiyarta take mishi.
D'uk inda tai K'allonta yake, sam tun jiya har yau
baida walwala, sai yaga ma kamar shi kad'ai
yake kin auren, dan har wani wasa ta d'au abun.
Turare take fesa mishi, kamar kullum taja baya
tana yaba mishi k'yaun da yayi, sai d'ai wannan
karan ci kanki bai ce mata ba, d'uk yadda tai
haka yake binta da ido.
Muryar y'an gidan Angwayen ne a parlour kan
wai sunzo tafiya dashi.
Takalmin shi sabo da jiya tasa Muh'd ya siyo
mata "half cover" takai gaban shi zata sa mishi,
cikin zafin nama ya dagota cikin masifa, cikin
t'sawa yace "Mey kika d'au abin ne? Wasa?
K'arfa ki mayarni yaro... Gaba d'aya ya burkice
mata.
Murmushi ta k'ak'alo na dole, tare da d'an zame
hannunshi tana fad'in, "relax", sai ta sa hannu
kan maballin wuyar rigarshi, har yanzun yana
mat'se da ita, "yau fa ba ranar fad'a bane Dear,
muje ana jiran ka a parlour.
Hankad'a ta yai kan gado,cikin fusata ya bud'e
kofar ya doko mata ita.
Da sauri ta tashi tasa sakata.
Tuni ta zame kasa ta cire d'aurin dank'walin data
sha, ihu zata kurma ta tuno basui nisa ba.
"Wayyo! Shi kad'ai ta iya furtawa,kan tai ko'k'arin
tashi, tuni ta fara ganin jiri,ba shiri ta koma ta
zauna, sosai tai k'arfin halin kin nuna damuwar
ta gaban Ahmad, da rarrafe ta hau gado, tuni
wani irin kuka mai matukar daci yazo mata...
"Shikenan ita, ta faru ta kare mata.
By
Feenat Ja'afar.
9/29/16, 2:47 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 37_Batta da mai
lallashinta kusa,saboda haka sai da tai mai isarta
tukun ta samu nutsuwa. A hankali ta daga kanta
zuwa ga agogon dake manne a d'akin na hutansu
suna k'allon juna. Sai tai lamo tare da kura ma
agogon ido,(10:50am), tasan d'uk inda suke
yanzu an d'aura na Maryam da Muh'd k'arfe
goma, kenan saura minti goma a d'aura na
mijinta? A hankali ta yunkura ta tashi,sai ta
furzar da iskar bak'inta ta k'ada kai, kaya ta hau
cire wa, d'uk k'walliyar ta goge da kuka. Bandaki
taje,cikin sauri tai wanka ta fito ta hau shiri,
sosai tai k'walliya kamar ma ita ce amaryar, sai
ta bud'e "wardrobe" d'inta cikin kayan da ta
tanada a fitar bikin ta hau zabi. Akan wata
dakakkiyar shadda ta t'saya fara ce,tasha zubi
da zare "Orange" da "blue" "gown". D'inkin yasha
"stones work" mai k'yau da t'sada, Kai ta kama
tattare achan kasan keyarta kan ta kamashi da
"ribbon" ya had'u waje d'aya a bayanta. Cikin
nutsuwa ta zira rigar kan ta t'saya gaban madubi
rike da dank'wali, ta baya ta d'auroshi, yadda
gashin zai shiga ya fito ta t'sakiyar d'aurin. Nan
da nan komai ya ji, sarka da "bangles'' had'e da
zobuna sun hau. Turare ta fara feshi, had'e da
murmushi lokacin da ta k'alli kanta a madubi.
K'warai ance in kana da k'yau, wai ka kara da
wanka, ita d'ai Pretty tanaji da d'an k'yaun nan
nata wajen kara k'wask'wareshi ta dawo mai
k'yau. D'akin ta g'yara kan ta fito parlour ta
kunna "burner", dirin mota taji, a hankali taji
gabanta ya fara fad'uwa, kila har an d'aura an
dawo... Da k'yar ta iya seta kanta ta had'iye
kukanta. Har tai hanyar d'aki taji Fatee na
k'wada sallama. Da fara'a ta juyo tana amsa
mata. Baki Fateen ta rike, "inye, ka ga uwar gida
a gidan AAA.. Kingan ki kuwa? Fuska ta K'awar
tana murmushin k'arfin hali. Fatee ta karaso
dak'yar tana tura ciki. "Allah ya kawo AAA
yanzun, na tabbatar za kisha k'arin angwanci,
kai! Ke ko a jikin ki koh? K'allon Fateen take,
tamkar ta sau kukan bak'in ciki haka take ji, wai
ko a jikinta? "Ki bari ka'r na huce tawa haukar
akanki da cikin ki.. Dariya kawai ta hau mata
tamkar taga shasha, kawai sai ta zuba mata ido,
ji take kamar ta rufeta da duka. Sai ta juya kanta
chan gefe kuka na shirin zubo mata, "wato ke da
zaki taushi zuciyata, ke kike min dariya ma...
Cikin dariyar keta Fateen tace "no,sorry, sorry,...
Sai d'ai fa taki t'sagaita dariyar, harda k'walla,
Fure na shirin fashewa da kuka ta t'sinkayi Fatee
na fad'in "Angon Furera... Da sauri ta rint'se ido,
gabanta ya cigaba da d'ukan tara-tara. Sai da ta
tabbatar ta had'iye kukanta tukun ta juyo had'e
da k'ak'alo musu murmushin dole. Shi da Salman
ne, sai d'ai kamar su ma dariyar suke,gogan na
ganin ta juyo ya g'imtse fuska, kawai sai taji
wani rauni yazo mata. Tun yanzu har ya fara
washe baki ni kuma yana had'en rai? K'wafa tai
a ranta, da gaske ne kam Namiji ba d'an goyo
bane ba. Ji fa yadda ya bar gida yana cin magani
amma daga d'aura aure har ya ware,ita kad'ai ya
dake wa. "Sannun ku da dawo wa, murmushi
Salman yai, kan yace "kinga taso mu tafi kan
wannan ''nuclear bom'' d'in ya tashi damu Batool.
Harara ta dan sau musu kan ta d'auke kai, sai
dai ko ita taga bala'in d'auriyar ta. Tashi Fateen
tai tana dafa cinyoyin ta, har yanzun dariya take
a ciki ciki, "toh K'awa, sai munzo d'anna kirji
anjima. Yake tai mata, suna dariya suka fuce ita
da mijin. Fure fa ta cika tai bamm! Kiris take jira
ta fashe da kuka. Kan maigidan ta dawo, kawai
sai taga yai d'aki ya barta, sam ba fara'a a
fuskarshi. Kai ta k'ada, sai ga nan wasu hawaye
masu d'umi sun zubo. "Wato ni AA zai manna
ma? Dak'yar ta iya tashi tai d'akin cikin goge
fuska, tana k'allon kiran Aisha da Adama taki
d'auka, gani take yau kowa ya t'saneta, sai d'ai
kana k'allonta kasan tai kuka. Jingina tai a jikin
kofar tana k'allon yadda ya t'saya a gaban
madubi yana kunce "link" d'in hannunshi. K'allo
d'aya ya mata ya d'auke kai zuwa ga abinda ya
ke, d'uk sai ta kara jin ta samu karaya. D'uk ta
marairaice fuska. Karasa wa tai gun da yake kai
a kasa taki duban shi, d'ayan hannun ta ruko
tana tayashi cire wa,ido ya zuba ma fuskarta
yana dan kunshe dariya ganin yadda ta
marairaice. Jin burbushin kunshe dariya yasa ta
d'an dago tana k'allon shi, suna had'a ido ya
kasa jurewa,dariya yake irin ta ketar nan, kawai
sai taga an ma mayarta mahaukaciya, cikin fushi
ta y'ar6ar da hannun da ta rike ta ta turo baki
tana shirin sakar kuka. Maimakon ya t'sagaita
dariyar tashi kawai sai nunata da hannu harda
rike ciki, tuni k'wa sai kuka ya k'wace mata, bai
nufa ba kawai ya ji tana k'wada mishi pillow ta
ko'ina ko zata huce takaicinta. By Feenat
Ja'afar. 庐NWA. Feenat.mywapblog.co
9/29/16, 2:48 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 38_Karewa yake,yana
mai cigaba da dariyar, ganin ba gajiya zatai ba
yasa ya fara ko'k'arin kar6ewa ya rukota, tun
tana tirjewa har tai lumm yana jijjiga ta tare
fad'in sorry,sorry. Dak'yar ya samu tai shiru sai
ajiyar zuciya take. Kanta ya dago, sai ta rint'se
ido d'uk k'walliya ta baci, sai ya sa hannu yana
goge mata hawayen sannan ya cigaba da jijjigata
da mata kirarin da ke sa ta nutsuwa. Luff,kake
ji,ba ko shesshekar, sai yai murmushi, shi kad'ai
yasan lagon Prettyn shi. "Pretty"... Ido rufe ta
dan mot'sa, sai yai murmushi, "you know.. "My
destiny is taking me where my love is. "Kin riga
da kin tare ko'ina nawa Furii..har ma ban iya
k'allon wasu mata a mat'sayin sun isa balle su
kamoki,cos I can see only one thing..hear one
thing..and think about one thing... That you
pretty.. Ido ta bud'e, sai ga nan hawaye ya
zubo,k'allon cikin idon shin take,so take ta gano
akasin zancen shin,amma ta kasa.. Ko haka ya
barta tasan yai mata lallashi da son shi, sai d'ai
kan ta farga taji dan hayaniya a kusan k'unnenta,
kamar kuma na d'aurin aure a waya yai
"recording". Sai ta mat'se ido,dan jin maroki na
fad'in sadaki kamin yace "na auren Rukayya da
Nasir.... Da azama ta bud'e ido tana k'allon shi,
gira ya daga mata yana murmushi.. Da sauri ta
karbi wayan ta kara taro wa, abu d'aya ta kara ji,
sai ta k'alloshi wai kuma ta hau kukan dad'i.
******"""" MU D'ANNA BAYa.. Tun bayan fitar
AAA da ang'waye dan halartar d'aurin aure suka
sauka gida inda za'a taru a tafi nasu Muh'd. Gida
ya shiga,"direct" yai d'akin Mama, ganan y'an
biki wasu a "parlour", su Ummi yaga,ya tambaye
ta Mama, sai tace tana bangaren Abba, sam
itama haushin za ai ma y'ar d'akinta kishiya take.
Da sallama ya t'saya bak'in kofa, daga ciki Abba
ya bashi izinin shiga, suna a parlour Mama na
had'a mishi "tea" d'uk yai wani iri, ji yake sam
bai zatan samu nasara ba. Bayan ya gaida su yai
shiru, Abba ya K'allonshi, "Har kun iso? Kai ya
k'ada, kan ya dago kai, da sauri Abba ya ajiye
kofin shayin, "Subhanallah, Abba na, kuka fa? Ido
Mama ta zuba mishi, kawai sai ya goge yana
kara zubo da wasu, tashi Abban yai, dan a duniya
ya t'sani ganin ran kowa ya baci a yaran shi bare
Ahmad t'dokarshi. "Haba Baba na.. Maza da
kuka? Fad'an wa ya ta6a min kai? Mama ya
k'alla, da mamaki itama take K'allonshi, kawai
sai yace shi baison auren nan, sam baison
Rukayya... "Abba yaushe akai auren namu da har
za'a kosa na kara aure dan bata haihu ba, nan
yai ta mishi, kan tana chan wai ya barta sai bori
take ta rufe kanta a d'aki tana kuka. T'sam
Abban yayi, sai yace Mama ta miko mishi
wayarshi. Momy ya kira, cikin k'ank'anin lokaci
tazo. Ganin Ahmad durkushe yasa tasan da wata
a kasa. Waje ta samu ta zauna, sai Abba ya
sanarta abinda Ahmad yace, tuni ta hau 90, kan
aure ba fashi, wallahi tunda har yau d'aurin aure,
yau ya nuna mata bata isa ba, yau harda Mama
ta balbale, tuni ta bawa Abban haushi, "t'saya kiji
Maryam, ki cire son rai, yaron nan kar mui mishi
dole, in aure yake bida zai ne in lokaci yayi, sam
ban zata ba had'in zumunci kike son kulawa ba,
kiyi hakuri, suma zasu haihu ne, amma a bar
auren nan... Kuka Momy ta sau, yau wai an nuna
mata karshenta, sannan an nuna mata ba ita ta
haifi Ahmad ba.. Shidai gogan yai kasa da kai,
fatan shi komai ta fanjama fanjam, yai lallashi
daga baya. "Momyn su kiyi hakuri, sam abin bai
ba, ranar aure kace ka fasa... ''Rufan baki, ai da
saninki a haka, kuma dad'inta na haifa, aure yau
za'a d'aura da d'aya a wanda na isa... Sallamar
Alhaji Nasir ce ta kat'se ta, "lafiya kuwa Abba?
Hayaniya har t'sakar gida fa... "Yauwa Nasir,
shigo, cewar Momy,shi d'ai Abba da ido kawai
yake binta, "Momy kuka? Mey toh yai zafi haka?
"Komai nace kawai kace toh Nasir,, hawaye ta
goge, "ina son ka auri Rukayya, ka fanshen bak'in
cikin da ake son dasa min akan Ahmad.. Da
mamaki ya k'allo su Abba, suma shi suke k'allo,
"haba Momy, aure fa? Ni? Kai za... "Ban san
musu Nasir,in dai ba kana son ku hallakani bane..
Kawai sai Momy ta hau haki.. Asma ta mot'sa,
da sauri suka rukota, Nasir dama ya sani yake
bai shigo ba t'saut'sayi ya fad'a masa.. Haka
yanaji yana gani ya yarda dan Momy na fad'in in
wai bai yarda ba wallahi zata mutu...Lol Ko su
Rukayya basu san zance ba sai da aka d'auro
suka ji, dan chan gidan su akaje. Bori ta hau
yiwa Momy kan ya za'a ta mata haka? Tana
k'wance asmar ta d'an saketa take bata hakuri.
Fur Rukayya tace batasan wannan ba, mey zatai
da tsoho, dan farin gidan, tuni ta tattare tai gidan
su tana kuka. ********************** Da sauri
Fure ta ruk'unk'umo abinta tana kukan murna, sai
kara kakank'ameshi take har tana shirin fad'arsu
kasa sai sukai kan mai laushi. Karan nan bai
hanata ba, dan yasan na murna ne, sai ma yahau
tsokanarta da fad'in, "haba uwar gida, yau fa ba
ranar kuka bace... Dariya ta hau yi kuma kuka
kuka. Sai ya zame dank'walin tare da mirgina ta
kasa suka zuba ma juna ido, mey zata ce da
abun nan? Lalle Allah bai had'a maka zafi biyu,
gashi an so a muzguna mata Allah bai yarda ba,
sai ta hau matso hawaye. Kanshi ya d'aura a
kafad'arta yana goge hawayen, sai ta hau kuma
sunne kai cikin kunya. "Sosai bayan na fita zuwa
kawai zanyi na auri Rukayya tunda naga ni kad'ai
nake k'ida na, sai d'ai ina fita na t'saya a bak'in
kofa, ina ji kika sa key kika zube, wai kuma harda
kuka, kinyi dauriya fa, ko irin y'ar haukar k'aryar
nan da mata suke ke baki ba.. Hakan ya nunan
ta ciki yana cinki, kawai sai nai jahadi na tunkari
yakin dake a gaba na... Kat'se shi tai ta hanyar
d'aura "lips" nata cikin magand'ar sa tana jin
kamar da haka zata biya shi. By Feenat Ja'afar.
Like 路 Reply 路 Report 路 Apr 30
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 39_Lokaci sosai suka
d'auka, kan a hankali ta fara ko'k'arin zame
kanta ido rufe,shima nashi haka, "thanks" shine
abinda ta furta, sai ya ware ido cikin nata, lalle
yau ya biya ta ba kad'an ba. Tuni kuma ya hau
tsukanarta tana dariya.. A mota suke,yau shi ma
zai kaita gidan bikin, hannunshi d'aya na nata
kawai ta juyo tana ta aika mishi murmushi yana
k'ada kai. Lalle kishi masifa ce, sannan batasan
haka son AAA ya kai ba cikin ranta sai yau da
ake neman a k'ak'aba mishi auren dole. Hannu
yasa yai tagumi yana k'allonta da murmushin
yadda ta zuba mishi na mujiya. Kawai sai taje ta
lafe tana d'an mishi dariyar kauna,t'sam ya
rukota yana sauke ajiyar zuciya. Yau d'aya ya
kara tabbatar da son da Pretty ke mishi. Dak'yar
ta dago tare da d'aukar wayanta, hannu ta daga
mishi, tare da fad'in ''Bye... Sai taji yai shiru yana
k'allonta kawai. Ta kara fad'in "hello", a hankali
yace "I love you.. Kai ta k'ada tana murmushi,
sai ta k'arkata kai da fad'in "I know... Cikin
shag'waba, bak'inshi ya nuno mata, ba gardama
ma ta nashi mai zafin, tare da fad'in "bye" ta suri
jakarta zuwa waje, dan tasan in ta biye mishi a
motar nan zasui ta zama. Zagawa tai ta
bangaren da yake, ta daga mishi hannu, kai ya
leko, "Remember that...Nothing gonna change
my love 4 you... Sai ta k'ada mishi ido tare da
d'aura jaka a kafad'arta.. Tace "really? Kai ya
k'ada, tare da jero Nothing..Nothing... Hannu
tasa a bak'inta tare da d'an wata munafukar
dariya, sai ta manna wa hannunta "long kiss''
Muahhh... ta nuno shi da hannun "love you... Da
farin ciki suka rabe, har sai da ya kule kan ta
k'ada kai ta shiga gidan su Umma. Da gudunta ta
karasa tana kiran su Adda da Aisha. Tuni suka
fara mata barka,reshe ya juye wai da mujiya.
Fatee ce ta kira ta, kan itama gata a hanya
bayan azahar, tana ta mata dariyar keta kan wai
d ansha da ita, ai ta fad'a mata taji a jikinta
auren nan babu shi, itade murmushi take kawai,
amma tasan da k'yar ta t'sallaka rijiya da baya.
Sai dai kuma ta tushe k'unnenta a gun su Momy.
Lafiya aka gama biki, sosai sun ma Maryam
bajinta har ta ninka Fure, kayan kitchen guda
Fure ta d'au nauyi, Ga nan AAA ya ma su Umma
gudunmawar kayan abinci da drinks, dan fur suka
ki k'ar6ar kud'inshi, Abba d'ai ya zama d'an k'allo
da Umma. Aisha Bedsheets, Ya Suleiman kam an
kafu sosai, d'uk kayan parlour shi yai,sosai ya
ka'r mata nera, kamar kullum yau ma kawu ya
d'au nauyin gado, ganin haka yasa ya sai mata
babba mai t'sada da k'yau. Koh y'ar gidan wani
mai kud'in karshenta kenan. Amarci sukaci ba
k'arya a gidan Hassana, yanzun ne Muh'd yasan
yai auren so da tararaya, sai yanzu yasan sirrin
dake cikin auren y'ar masu karamin k'arfi da
suka rena. A gun Momy kuwa, kowa ta d'aina
kula shi dan a ganinta an mata babban
wulakanci. Kullum sai Ahmad yazo gabanta
neman gafara, yau d'ai har da d'an guntun
hawayenshi dak'yar ya shawo kan Momyn. Ta
bangaren Rukky kuwa tuni babanta yace bazata
zauna mishi gida da aure kanta ba, su Momy su
ne iyayen ta,dole haka tanaji aka yayimeta aka
kaita gidan Nasir. Hassana na gida, fur Muh'd
yaki zuwa biko, yace ai ba shi yace ta fita
ba,zata iya dawo a d'uk lokacin da taso, ganin ba
sarki sai Allah yasa ana wata da bikinsu ta
tattaro ta dawo,sai d'ai ganin Maryam a gidan ba
karamin bala'i ta tayar ba, a fafur sai d'ai ya
sauya mata gida. Shikam yace amarya tace had'i
take bida. Komai yi suke a gaban Hassana,haka
zai ta biye wa Maryam suna guje guje a parlour
akan abu kad'an. Hassana sai a ta6e
baki,"mahaukata kawai.. Sam Maryam bata bin ta
kanta, sai d'ai da taga zata shiga gonarta zata
taka mata birki. Sunan Huwaila ake yau, wannan
ce rana tafarko tun bayan auren su Maryam da
Fure suka had'u da Familyn gu d'aya. Murmushi
kawai take, jin ana chakarta kamar kullum,ga
rashin auren Rukayya ya dad'u,tasan batta bak'in
komai. Muryar Hassana tafi ta kowa tashi a
d'akin maijegon. D'ai-d'ai su Maryam da Ummi na
shigowa suka t'sinkayi Hassana na fad'in "bar
mat'siyaci, nima ana chan anga guri ana ta
6arkan hauka, cewar Hassana. Da sauri Maryam
d'in ta karasa d'akin, sai da taje d'ai-d'ai kan
Hassana tukun ta k'alli Fure,"sha kurumin ki
sister, sai tai gefen Hassana da hannunta tukun
tace "dan tuni t'siya ta kare kan t'sohon nan na
gida mai kud'in LUKUD'I ... Wanda da iyalanshi
su ci k'wada K'adangarun BARIKI suci... "Sannan
t'siya ta kare ga uban yana da kud'in, amma in
ya dire buhu masara, daga ranar ba sauyin abinci
har sai ta kare. Sai ta k'allo Hassana, "toh indai
kikazo nan, toh k'wa t'siya ta kare a gun ubale...
A tunzure Hassana ta mike, zatai kanta, da sauri
Maryam d'in taja baya tana k'allon Hassanan
kamar taga kashi, ilahirin d'akin sun zubawa
Maryam ido suna k'allo baki sake, ''ni fa t'siya ta
da y'ar gidana akuyanci, yanzu sai fa kice zakiyi
dambe dani? A kuma cikin taron jama'a.. "Toh
wallahi ki iya bak'inki... Chan ta mat'sa kusa da
Ummi ta zauna, tai banza da Hassana wacce ke
nad'e tabarmar kunya cikin jama'a. Har dariya
Aunty A'i yau tayi, lalle wai "GABA DA GANTA...
Tun zuwanta gidan Maryam d'in ta tarar da
fad'an su da Hassana tasan za'a buga da
Maryam. Yayinda maijego ta ta6e baki, badan ta
kanta take ba yau da ta takawa Maryam burki.
D'uk da tabbas batai ma Hassana sharri ba, dan
fa sai da ta ciwo maganin zama da ita ka'f kan
ta yarda a had'a su zama tare, tai alkawarin d'uk
d'an uban da baiji kunyar taka mata y'ar uwa ba,
toh itama bazata ji kunyar take shi ba. Ita kam
Fure kasa tai da kai tana murmushi, tabbas
tasan wataran KARE na yawo, KURA na yawo
tasan dole za'a a had'u. Batajin da wanda
Maryam zata dagawa K'afa a ka'f Familyn su
Huwaila. Lalle kam,dole ta zama y'ar k'allo, dan
k'wa badai ita ta takawa Maryam burki ba sam.
Fatee ta haihu babyn ta mace, da zumudi ta
gama abinda zata kai mata tai gidan, dan ta ce
an sallame su. "Drama" taje ta tarar, wanda
sosai taci dariya. Fatee na band'aki taji sallamar
y'an gidan su Salman, da sauri ta wat'sa jin sun
shigo d'akin da ake shirya baby. Cike da murna
suka zauna a gama su k'ar6i baby. Da d'aurin
kirji ta fito, nad'e da towel a kanta, d'ai-d'ai za'a
basu Baby da sauri ta karaso ta shiga t'sakani,
"Wa? Ai wallahi na rant'se ba shegen da acikin
ku zai d'au y'ar JUYA.. "Dallah mat'sa min daga
nan, ta warce y'arta ta d'ane gado tana bala'i.
Gaba d'aya sun kasa cewa uffan, Fure da tazo
ganin ikon Allah yasa ta ma kasa sallama, Ashe
da gaske FATEE take da tace ba mai d'aukar
y'arta acikin k'annen Salman sai d'aya? "Ido ko
kunya babu wai kunzo ganin Y'a? Toh g'wara ku
d'au fagon wani gu ku barmin gida, tuni wasu
suka fusata, har sun manta, ana haka y'ar k'anin
Baban su tazo da y'an gidan, jin yadda Fatee ke
ma dangin mijin wankin babban bargo yasa taja
tai shiru, aikwa sai da ta wanke ta tas! Kan d'uk
taji sanyi. Zuciya sukai suka fita suna ta jika y'ar
tasha.. "Eh zan jika...aje d'ai, gaiyar na aiya.
Salman sai da yazo bada hakuri,yana dari dari,
ganin yadda take cika, ba shiri yai shiru. Suna
zuwa suka sanar da Umman su Salman d'in, da
mamakin su sai su ka ga tai dariya. Sosai Fatee
ta burgeta, sai ta k'allo su, "kuna nufin kunji
haushi? Kai suka k'ada mata, sai tai murmushi,
"da zaku san adadin shekarun da na d'auka kan
na haife ku da baku kara kiran wata JUYA wai
dan bata haihu ba, na zuba muku ido ne, dan
nasan dole wataran zaku d'au darasi. Kowa
k'allon kowa yake, su d'ai tun ba yau ba suna
mamakin yadda Umman su ta t'sufa kuma wai
ya Salman ne d'anta na fari. By Feenat Ja'afar.
庐NWA. Feenat.mywapblog.com
9/29/16, 2:49 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 40_Rayuwar tana tafiya
ma Fure cikin godiyar Allah, domin a kullum ta
Allah tana matukar samun cigaba a rayuwa. Bata
da tawaya ta ko'ina ta bangaren jin dad'i ko
zamanta da mijintan, sai d'ai har yanzun Allah bai
nufi samun ciki ba, a kullum batta kalmar fad'i
ga Allah da ya fice "ALHAMDULILLAH" domin ya
bata d'ukkan farin cikin rayuwa... Tawaya ta
rashin D'a, bazata tai ma Allah butulci
ba..InshaAlllah, Abadan. Ga wani karin farin cikin
budi da ya same ta,AAAn ta ya bud'e mata
"Restaurant" nata na kanta. Jere suke, anyi
rubutu cikin "bord" d'aya da symbols.. "AAA
pharmacy & stores Ltd. Yayin da nata dake
makotanshi yasa mata "Mr's AAA Restaurants"
tamkar tag'waye abin g'wanin ban sha'awa. Toh
mey zata ce da Allah? Sai Godiya. Ajiyar zuciya
ta sau, lokacin da ta kara g'yara mak'wancinta
tana mai zuba ma AAAn ido wanda ke murza mai
a gaban "mirror" yana mai dan k'allonta. A zahiri
shi take k'allo, amma sam hankalinta yayi kan
dumbin Alkairin mijinta gare ta. A hankali ya tako
zuwa gefenta ya zauna, tai kur'i da ido ba ko
kiftawa. Ido ya zuba mata, ba t'sammani sai ga
nan siririn hawaye ya zubo bisa kuncinta. Hannu
taji a fuska ana goge hawayen, cikin nutsuwa ta
waiwayo da duban ta gare shi, murmushi yai
mata, kan cikin zancen karatun kurma ya tada
kai halamar mey ne ne? Murmushi tai,kan ta
k'ada kai halamar babu, sai ta matso tare da
d'aura kanta kan kafafunshi tana k'allon
fuskarshi,sai ya kai hannu yana mai tattare
gashin da ya bazar mata, sai ta ruko hannun tare
da rint'se su cikin nata tana k'allon shi. D'ayan
hannun takai fuskanshi tare da murmushi tana
shafo ta,shikam murmushi yake mata,cikin
sanyin murya ta hau mishi godiya bisa ga
k'yautatawar shi gare ta.... "Life is really not
worth living without you! You make me feel so
special and complete! I can鈥檛 find words to
utter,but I just want to say 鈥淭hank you and I love
you much more Dear... JazakALLAH. Ajiyar
zuciya ya sau, tare da k'ada cikin da jin dad'in
kalamanta, cikin salon shi dake sata taji tamkar
ita d'in "Queen" ce a "Universe"... Tuni ta sa
mishi ido kawai tana k'allo,ganin d'uk yadda tai
taga tafi AAA iya lafazin a fagen kaunar shi,sai
d'ai ina,tuni ya mata nisa. Dariyar suke,lokacin da
ya bud'e mata''bott" tana d'aukan k'wandon
abinci,sam bazaka ce su ne suka shekara 4 da
aure a tare ba, sun fi kama da irin sab'bin auren
nan dake ji da junan su. Mika mishi d'aya tayi,
kamar kullum ta d'au na Momy. Chan ta fara
yada zango kamar kullum, suna "parlour" ta tarar
Huwaila na kuka tana fad'in ta gama aure.. Suna
jin sallamarta sukai shiru, waje ta samu, sai ga
nan Rukayya ta fito a kitchen da abu a hannu,
kamar kullum cikin girmamawa ta gaida Momy,
sai da ta k'au da kai tukun ta amsa da "lafiya,
kan Aunty Jidda tazo, ita kam harara ma ta sakar
mata, su kam sauran ba wanda ya tanka ta, shiru
kake ji ba mai cewa uffan. Takan rasa a rayuwa
mey ta t'sarewa bayin Allahn nan, sam yadda
suka ki jininta ko Maryam da bata barinsu basu
t'saneta haka ba. "Mtsww.... T'saki Rukkay
taja,kan ta samu gefen Aunty Jidda ta zauna.
"Gaba d'aya anyiwa mutum dabaibayi duk an
hanashi rawar gaban hant'si. Ta karasa tana
y'atsine fuska, murmushi ta mata,kan tai kasa da
kai, Aunty Jidda tace "wai ni ba naji an bud'e
Restaurant da zummar nata ba? Hala tun yanzu
ya fara raba gado tunda ba D'a bare kwai? Baki
Momy ta ta6e, "shi fa ya sani, ni ina ruwana, su
had'u su talautashi ma shi ya sani. Kasa tai da
kai kawai tana jin su, tana jin Rukky ta amshe..
"hmm, matsiyaci kuke ji,ai bai iya samun gu ba,
sam yadda zaki san abin nan da agumau yadda
yaya ke rawar kai akanta, wallahi shi yasa bazan
ta6a harka da mat'siyacin mutum ba, sam.
K'allonta take, sosai nata sai ido, Fure lalle Allah
ya yarfa wa zuciyar ki hakuri, dama Maryam na
gun. Tamkar masu huce haushin mijin Huwaila a
kanta haka kowa ke mata, sai d'ai wai harda
Huwailan a zaginta? Abinda da mamaki, indai har
zata kirata da haka. Ita d'ai murmushi ne kawai a
fuskarta, sai ta janyo "basket" d'in abincin ta
mika gaban Momy tace ta tafi, ba wanda ya
tanka,sai ma t'saki da Rukayya taja mata. Sai da
ta t'saya a gefen "corridorn'' ta goge hawaye kan
ta karasa gun Mama. Anan ne kawai ta samu
farin ciki, mama tana ta sa mata albarka akan
abincin "weekend" na kullum. Abba da yazo
bangaren kamar kullum weekend sai ya tarar
dasu Furen, shima yaba mata yake akan ko'k'arin
iya girki dasu duk k'wana uku na weekend, sosai
Fure ta shiga ranshi, gasu da ladabi ita y'ar
uwarta.. Ka'f sirikan gidan daga kansu ne kawai
masu sanin ya kamata. Da dare ta biya dubo
Maryam da cikinta ya isa haihuwa. Ba ai k'wana
uku ba k'wa ta haihu,ta samu babynta namiji. Da
murna tai d'aki dan sanar da AAA, sai gashi
shima yana shirin sanarta har suna g'ware,
"Maryam ta sauka... Sai suka sa dariya jin sun
had'a baki gun albishir. Sosai Muh'd ke d'aukin
zuwan babyn nan, yayin da Hassana ke ta cika
dan wai ita yara mata ta haifa har uku,gashi har
an fara kiranta da "UWAR MATA.. Amma ga
amaryar shi tana zuwa har ya bata namiji a wata
goma.. Ranar Maryam tai dariya kamar ta mutu,
kai rashin ilimin Addini ne ma masifa ce, sam
yanzu ita gani take Hassana ta kunce. Suna a
parlour ana g'yara baby Hassana ta fito,gobe
suna fir taki zaman parlour, jin yadda ake ta
shigo da abubuwa. Fatee da Fure suka bita da
k'allo, sai kunshe dariya Fatee take,dan ganin
yadda Hassana ke hararar baby da uwar shi. Da
gan gan Fatee ta fara "Accountant" ba, yaro mai
goshi, sosai kazo da azziki. Baki ta ta6e, kan
cikin haukarta ta fara ma Jidda dake kusanta
"Jidda y'ar gatan Abba koh? Sai Jidda ta k'ada
kai, cikin zance ta kara da cewa, "Dad'in abin na
haifa, ba o o bace, nasan yau da Jidda ta iya
mota,nasan da dadyn Jidda ya mallaka mata
ita... Fatee ta k'alli Maryam, kawai bata nufa ba
sai ji tai sun sau mata dariya harda shewa da
tafawa, kamar wanda suka had'a baki wajen
fad'in "wa yaga takai takai,,cikin dariyar mugunta
Maryam tace "uwar Jiddan ma tai ko'k'arin
mallakar ta kamin nan ita Jiddan... "Wallahi ban
so ba,da tuni na mallaka.. Baki Fatee ta ta6e,kan
tace su shiga ciki kawai, ita d'ai Fure nata ido.
By Feenat Ja'afar.
9/29/16, 2:50 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 41_Suna ya kayatar,
sosai maijego ta fito da yayarta, baby yaci sunan
Abba,an ka'r naira sosai, da yamma kamar kowa
aka kawo kayan maijego da baby na mey suna su
Aunty Jidda. Har kasa Fure ta zamo ta gaida su,
Maryam tana daga gado ta gaida su sam ba
fuska. Cikin fara'a suka amsa, Ak'wati biyu Aka
sheko musu, komai na k'arya da nuna su sune,
ganan wata katuwar leda da tarikicen su
pampers da da sauran su. Fure da Ada da Fatee
na duba kaya Maryam tai waje gun amsa kira.
Huwaila da ke kusan su Fure dake ganin kaya
cike da izgili ta k'allo Fure, "tunda y'ar uwa ta
kot'se sai a zuciya bana a diba.. Chak Maryam
ta t'saya wacce shigowarta kenan da masu duba
kaya, a fusace Maryam ta karaso, "Sa'a kike
ko... Da azama Fure ta tashi ta toshe mata baki,
sai ta girgiza mata kai. Sai d'ai kan ta farga har
Fatee taja t'saki. "Haihuwa ai kai inda ake
nemanta itace haihuwa a gani na.. In ta wuce
wannan, wallahi na yarda a kiramu da JUYA... A
wulakance Huwailan ta k'allo ta, "ke kuma a
suwa? Wai kare da gudun layya.. Mtsww, "Allah
ya fissheni zama JUYA. Dariya Fatee tai,kan tace
''oho d'ai, dan dake da babu agun mijin d'uk d'aya
wai karuwa ta haifo shege. Tuni ta tunzura
ta,har ta soma zagege su Aunty Maryam da
Jidda suka shigo jin ba'asi. D'aya ta fad'a sai
Fatee ta mayar mata goma, ita d'ai Fure ta
damke bak'in Maryam gam,dan yanzu tasan sai
ai baram barama ranar suna. "Ki taso toh mu tafi
ke Huwaila, banga t'saran yinki agun nan ba.
Cewar Aunty Jidda. Da t'saki Fatee ta bisu, tana
fad'in "a sauka da nauyi. K'allonta Aunty Jidda
tai,kan ta nuno, "ki shiga taitayinki dani,ba
JUYAR bace ita? Ta fad'a... Fatee tace "oho d'ai,
nima d'ai na fad'a, ka haihu inda ake mararin ta
ba inda aka maishe ka JUYA tafi ka mukami ba...
Janta Huwaila tai, tana "Aunty bar mahaukaciya,
ba laifinta bane, da k'arfi Fatee tace "Dawan'au
ce ma ni. Sai da ta tabbatar sun fita tukun ta sau
bak'in Maryam, kusan kowa na parlour, sai su
Ummi da kawayenta, suma ana farawa sukai
waje,dan taki jinin taga ana ciwa Fure fuska a
gabanta, dan d'uk yayunta ne. "Aunty Fatee kin
mun d'ai-d'ai wallahi, cewar Maryam, "sam Ya
Furera tamkar sun dat'se mata baki haka take, a
kusa da Fatee Fure ta zauna,cikin marairaita
tace"Fatee Aunty Jidda ce fa? Yayar su AAA..
Baki ta ta6e, "ke kika san wannan, ai d'uk tsohon
da baiji kunyar hawa Jaki ba,toh k'wa Jaki ba ya
ji kunyar nana shi kasa ba. Adama tace "sosai
kuwa. Sai ga nan Hassana ansha d'auri tazo, "ina
tajin hayaniya,da fatan lafiya? Harara Hassana da
Maryam suka k'wad'a mata, kan Maryam tace
"ba'a sani ba uwar gulma, Fatee tace
"Shishiganatu ba. Jiki sali6e Hassana ta juya
Allah sarki ta koma. Ita d'ai Fure sam bataji dad'i
ba, ta kuma sanarsu in dan ma ita sukai toh
wallahi basu burgeta ba, nan suka chake ta,kan
wai tsoron su take, "shi yasa kowa ke cin kashi
akan ki ai. Cewar Fatee. Aisha kam tai shiru, dan
sam ta t'sani hayaniya. Sai ta kama hannun Fure
suka fita su Fatee na kiran matsorata. Aisha ta
k'allo Fure dake kuka acikin motar da suka shiga.
"Ki kara hakuri Furera, wataran sai labari, ki
d'aina barin k'ananan maganganun su suna miki
tasiri, ak'wai Allah, ki sa ranki a inuwa, Allah yai
alkawari ga d'uk bawanshi ba wa d'uk wani abu
da ya tauye shi aka goranta mishi shi, mat'sawar
k'wa baka samu ba, toh ka d'auka wannan abun
ba alkairi bane gare ka da rayuwar ka. "Kar kisa
a rai,g'wada ki rama da ki barshi a ciki yazo yai
miki illah. Kai ta k'ada mata, "wallahi ban ta6a
da na sani akan hukuncin Allah ba sis, abu d'aya
na sani, d'uk ranar da hakan ta faru nakan ke6e
nai ta kuka,in na gama na share, ban kuma ta6a
fidda rai daga samun ra6o sam, sai d'ai bana iya
d'aure gorin jama'a, musamman dangin su AAA.
Sosai ta lallasheta, har sai da tace ta g'yara
fuskarta kamar ma ba ai komai ba, sannan kar ta
cewa su Maryam komai. Ko da suka koma k'ida
suka ji yana tashi a d'akin Maryam, suna shiga
Fatee da Adama na ta rawa suna bin kid'an Ladi
mai kid'an k'warya kamar basu ba. Murmushi
tai,sosai Fatee y'ar hau ce ita da Ada da
Maryam, sam ba zaka d'auka ba y'an uwan juna
bane. Suna ganinta Fatee ta kamo hannunta wai
ta shigo fili, ga nan y'arta sai k'yak'yala mata
dariya take daga zaune. Har gida karan nan ma
Momy tazo ita da Aunty Jidda suka sauke mata
ruwan bala'i. Lokacin AAA na d'aki yau tun safe
yake k'wance ciwan kai. Sama-sama yake jin
hayaniya, a hankali ya daga window, muryar
Momy da Jidda yake ji suna sauke wa Prettyn
shi tana ta fad'in suyi hakuri. T'sam yai bai ya
koh k'wak'waran mot'si, ya dace ya kawo
karshen kiyayyar da su Momy ke ma Furii,amma
ta ina? Tas Ummi ke sanarshi d'ukkan abinda ake
ma Fure kawo da gorin haihuwa. Lekawa ya
karayi, ga nan FURIIN ta duk'ar da kai kasa,a
ranshi yana kila ma kuka take... Sai ga nan
shima idonshi ya cicciko jin Momy na fad'in "ki yi
zuciya ki fita sahun JUYA toh.. Amma dole su
fad'a miki. Itama fit'sarun Maryam zani har gidan
tunda a dalilinta komai a afku,tun shigowar ku
dangin mu aka fara t'siya,saboda an yayimo
dangin t'siyar. Ya'yan makaniken mota.... Da
sauri ya sau labulen, tare da komawa kan gado,
bazai iya d'aukar jin wannan kalaman ga Furii
ba,tuni ya ji ciwan kai ya karu, shin Ina wai
Tauhidin su Momy yaje ne? Wannan tambayar
yau ita tazo kanshi, sai d'ai har suka gama
hayaniyar su bai samo amsa ba. By Feenat
Ja'afar. 庐NWA. Feenat.mywapblog.com
9/29/16, 2:51 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 42_Tamkar marainiya
haka ta takure kanta a parlour tana kuka mara
sauti,sai da tai mai isarta ta kad'e tai d'aki cikin
sand'a, a zaton ta har yanzun bacci yake,dan
tasan da idonshi biyu da yanzu ya taso gaida su
Momy. A.c ta rage mishi, kan a hankali g'yara
mishi bargo tare da ta6a kanshi, da dan sauri ta
wanke fuska gudun ka'r ya gane tai kuka, sai ta
fita kitchen. Da k'allo ya bita yana mai tausayin
ta had'i da karin kaunarta. Tabbas Furii tai sanyi,
sanyin ma na ban mamaki,dan shi zaya bada
wace ce Fure? Amma yanzun tai hakuri tana ta
cin jarabawar rayuwa. Har bazai tuna rana ta
karshe da tai pt a gidan ba,gaba d'aya ta
faiwalawa Allah, tai hakuri, amma ya rasa mey
yasa mutane suka gaza hakurin da tai, wace irin
zamani ne yanzu Allah ya kawo mu? Bargo kawai
ya cire yai tagumi. Sai ana kiran Magriba tazo
tashin shi, sai ta tarar ya ma tashin, sai ta koma
kitchen. Yaga har anci abinci bata ce mishi kom
ba, dare yai sosai, sai ma dan tad'in da take
mishi tana "massaging'' d'in kanshi a hankali.
Yasan kawai d'aurewa tai kamar kullum dan
kwanciyar hankalin shi. "Furii...a hankali ta
amsa,tana cigaba da abinda take, sai ya ruko
hannun d'uka tare da zago da ita suna k'allon
juna,tabbas yasan d'auriya take, amma har
yanzun bata dawo d'ai-d'ai ba. Kasa tai da
kai,ganin yadda ya zuba mata ido, hannayen su
ya rint'se, tare da g'yara zama kan gadon. "Are
you Ok?.. Kai ta dago tare da saurin k'ak'alo
murmushi, sai ta k'ada kai, wato ba d'ai zata
fad'a ba? Sai ya sau ajiyar zuciya, ya fara abin
da yasan d'uk rashin walwalarta takan dawo farin
ciki. Ido kawai ta zuba mishi dan jin kalaman
kaunar shi gare ta. Bata nufa ba sai ga hawayen
dad'i ya zubo, cikin sauri ta isa gareshi ta lafe
tana murmushi, a hankali taji komai na warewa
har ta dawo cikin nutsuwar ta. Tasan in da AAA,
sam ba ita ba k'wanan bak'in ciki, Son shi kuwa,a
ganinta zai iya mantar ta d'uk wani gi6i da ya
tare mata gaba.. Fatan ta yasa kaunarshi ta
d'aure, dan shi kad'ai ke samota ko ta k'auce.
Zaune suke a parlour suna firar duniya, ta tasa
kanta da cinyarshi a kasan lallausan darduma.
Ag'waluma ke a hannunta d'aya, yayinda d'ayan
ta rike lollypop,jin yai shiru tana ta zuba yanzun
yasa ta k'allo fuskarshi. Kawai ya tasa ta gaba
kamar wata TV da murmushi yana k'allon yadda
take kai alawar tana zance. Sai kai alawar bak'in
shi, ba musu ya k'ar6a. Da hannunta take bashi
itama ya bata. Ta kawo hannu zata bashi taji ya
rike, sai ta k'alleshi, y'atsunta yake dubawa cikin
farcen,sai yai dan shiru. "Lafiya?.. Kai ya k'ada
mata, sai ya tada zaune,duben ta ya fara, d'uk
da ba bangaren shi bane, t'sam yai yana tunani,
ita d'ai Fure sai K'allonshi take,ganin ya sauke
idonshi kan rigarta. Sai ya k'ada kai, "yau period
naki k'wana nawa ya wuce? Baki sake take
K'allonshi, dan abinda bai ta6a mata ba kenan.
"K'wana shida,lafiya? Murmushi yai, kan yace
"yana kaiwa haka dama? Sai tai jim,kan ta k'ada
kai, ''sai d'ai ya wuce da biyu ko uku.
"K'wadayinki na k'wana niyun nan fa? Kai ta
lang'wa6e, "dama ina yi ai,musamman in na kusa
farawa. Hannun ya kai inda yake k'allo, "nan fa?
Su ma haka suke? Sai ta dan harareshi, "sosai
sukanyi suma in zanyi.. Lafiya? Tafin hannunta
ya shafa yana k'allo, sai ya kai hannu gemunshi
yana shafawa tare da mata wani k'allo.. "Ke ma
fa kin sauya a um um... Bori ta fara,ganin yadda
yake ta mata t'siya, dariya yai, sai yace "ina
zuwa ke d'ai. Sai ya tashi yai d'akin kayanshi na
tarkashen aikinshi. Tunani take, itama fa tana
dan jin sauyi a tare da ita,d'uk abubuwan nan da
take k'wadayi yanzun, ba su take ba in period ne,
sannan... K'allonshi tai ganin yazo da pt da abin
da wani abu, a dirare take K'allonshi, anya yau
mutumin lafiyar shi kuwa? Duk sai wani fara'a
yake,hannunta ya kamo,sai ta tsura mishi ido,
"meye wanchan?.. Da sauri ta juya inda ya nuna,
"ahh..tace da sauri,jin an soka mata wani abu a
yat'sa,da sauri ta juyo dan jin zafi, tana ganin jini
ta hau kukan baci,hakuri yake bata, kan ko yace
ta t'saya yasan ba zatai ba. Baki ta zumbura,
harda dan hawayen karya, yana sakar hannun ta
hau yarfewa cikin lang'wai, sai yai murmushi ya
k'ada kai, tukun ya hau abinda zai, da kamar
minti biyar fara'ar fuskarshi ta karu, yayinda Fure
take K'allonshi tana dan yarfe hannu. Bata nufa
ba taji ya ruk'unk'umota har suna yin kasan
carpet, "I knew it.. Ciki fa, Allah Pretty...
K'wak'waran mot'si ta kasa,baki sake take
K'allonshi, kan a hankali ta furta "ciki?.. Kai ya
k'ada mata, "sosai, tashi muje lab, dagota yai,
kawai d'uk sai ta zama wata doluwa, da ido
kawai take binshi ganin irin bak'in da yake ta
washe wa. A lab ana ta yi da Fure, da k'yar ta
sa kanta a jikin shi kan aka sa syringe aka zuki
jini, y'an wajen sai dariya suke musu, ganin
yadda yasa cotton yana goge mata gun harda
hurawa yana fad'in sorry,ya rasa meye a allura
da Fure take kinta? Tuni sai ya tuna mishi da
wani lokaci achan baya.. Basu jima ba aka fito
da "result". Kad'an ya rage ya dagata sama ta ja
baya tana k'allon y'an cikin "reception" d'in, d'uk
sai taji kunya, Hannunta ya kama sukai
waje,amma bai iya jurewa ba sai da rungumota
cikin murna,tayashi kawai take, kan a hankali ta
k'ar6i result d'in, ganin abin da ke jiki yasa ta
kafawa papern ido ba ko kiftawa. A hankali ta
dago da dub'enta gare shi, ta kasa furta komai,
kai ya k'ada mata yana shafa cikin. Tuni hawaye
ya cika idon ta, "ciki?... Bata nufa ba taji ta fara
jika pepern da hawaye, janyota yai yana "oh no
Furii...murna za kiyi,tana shiga jikin shi ta fashe
da kukan dad'i, ikon Allah, Fure ta ciwo
POSITIVE. By Feenat Ja'afar.
Like 路 2 路 Reply 路 Report 路 May 2
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 43_Dak'yar ta saisaita
ganin wasu za su nufi lab d'in, hawaye ya hau
goge mata, tai kukanta yasan na dad'i ne, ko ba
komai yasan farin cikin FURIIN shi yazo. Allah ya
yi,Alhamdulillah itace kalmarta ta kullum a gun
Allah,domin ya mata gata masu yawa,shi yasa
zai g'wada imaninta gare shi. Tuni ta hau istigfar
bisa kukanta da tai tayi a chan baya. Jiyan nan
ta gama mishi maganar su d'akko Amal,kuma yai
murna. Tafe suke yana ta d'an turo ciki da kama
k'ugu tana mishi murmushi, sai ganan wata mata
da tsohon cikinta, kawai sai ta maka mishi
harara, da sauri ya d'ai d'ai ta, dariya Fure ta
hau, sai tabi matar da k'allo,ko ta zata ta da ita
yake ne oho. Suna zuwa gida ya d'akko ta a
hannu kamar wata Baby, Baba mai gadi ya
girgiza kai yai murmushi, sosai suke burge shi,
dan gidan su babu hayaniya. A gado ya direta
suna dariya,kawai sai ya t'saya k'allonta daga
k'wancen, sai tai murmushi tare da miko mishi
d'uk hannunta halamar yazo gare ta, ba musu
kuwa ya taho,d'uk sai tai mishi dabaibayi cikin
hawaye. Fatee ta fesawa, kan su Adda suka ji
bayani, alkawari tace ya mata, kan dan Allah kar
kowa ya ji in ya wuce Mama, tana son kawai ya
fito ne,za su fi dauk'in shi. Kai ya k'ada, yasan
tana son ma wa jama'a ba zata ne, kuma
InshaAlllah ba mai ji sai d'ai in ya fito su ga. "Kai
k'awata nai murna wallahi har ba iyaka, gani nai
bazan iya k'wana ba sai nazo ganin ki. Murmushi
tai kan tai gefe da kai. Hannunta Fatee ta kama,
"ki min maganin t'sagerun dangin Ahmad d'in nan
dan Allah... Ki rama abinda sukai miki,wallahi ki
hana ko wacce t'sageriyar babyn ki ko k'ya huce
takaicin baya. Kai ta k'ada tana k'allonta, "sis
Fatee da k'yar ne, kowa yai nagari dan kansa,
abu d'aya na sani,shine ba mai ji bare gani, sai
d'ai dake kinsan d'an duma ne. "Hana su d'aukar
D'ana bazai iya hucen takaici na ba, asalima
Batool, nai alkawarin d'uk wanda baizo ya ga
D'ana ba zan kai mishi har gida. Kai Fatee ta
k'ada, "lalle kina da hakuri, tab, wallahi ba wanda
ya isa nai mishi haka. Murmushi kawai tai. Sai
d'ai a daren fure ciki ya shiga 5 weeks ta soma
matsala,tamkar an jangamo ta. Washegari taje
ganin likita,sai taya AAA murna yake,kan ya bata
magunguna kan in ya cika 3 month tazo yai mata
"scanning". Tun daga wannan rana Fure ta dage
da godiya ga Allah da kuma gode mishi, sosai
take wahala da cikin,d'uk ta rame tai fari abunta,
dole wacce bata so aka kawo mata, wato y'ar
aiki. D'ai-d'ai da abinci ta d'aina yi, sai d'ai
kullum daga restaurant d'inta a kawo wa Baba
maigadi da mai gidan,ita kam sai d'ai Umma ta
dafo mata tuwan hat'si,shi kad'ai ke shiga, mama
kawai ta sani, shi yasa bata rabo da aiko mata
kayan makulashe, koh ta aiko Ummi tai mata
k'wana biyu. Har gida Mama tazo ta duba ta,tare
da mata adu'ar Allah inganta. Ba wanda yasan
da jinyarta a gidan sai su biyu da Ummi,sai Abba
da ya ga an d'aina kawo mishi "delicious" na
Fure. Ita kam Momy ko rashin zuwan abincin bai
dame ta ba, sai d'ai su Huwaila dake fad'in kila
ta ware su ne yanzun cikin kason ta. Fir koh
jajen rashin ganinta basui ba har yau. A haka har
ta raka wata ukunta. Sunyi tafiya da Abba
Abuja,yayinda yace taje kawai dan cika umarnin
likita. Hawaye take sosai a kan gadon scan d'in,
shikam likita ya ma kasa cewa komai, sai chan
ya nisa, a gaskiya kuna da sa'a a rayuwa ke da
Madam Fatima, haa'a.. Sai ya maida kanshi jikin
allon machine d'in. "Malikul kuddus kenan,
gaskiya ina da babban tukuici in na sanar da
"pharmacy" wannan abin farin cikin. Da sauri ta
girgiza kai, "A'a Doctor, dan Allah ka riken ya
zama sirrin mu, dan Allah... ''Assistance" ta
kusan su tace "amma wannan abin farin ciki ne,
balle ga mijinki. Kai ta k'ada, "na sani, sosai ma
kuwa. Murmushi likita yai, "na gane Madam,
InshaAllah pharmacy bazai ji batun nan ba, I
promise. Kai ta k'ada, harda godiyarta. Tana tafe
a mota tana kara yabo ga godiya ga Allahu
subhanahu wata'ala,lalle Allah gagara misali ne,
ikon shi ya wuci komai, kuka ta fashe dashi
sosai, sai ta nemi gu tai "parking", lalle hakuri
wani abun ne a matakin rayuwa. Hannu takai kan
cikin, sai ta rint'se ido, hawaye ya k'waranyo.
Tuni ta fara ma wa Allah kirari, a cikin k'arfin
mulkinshi da iko, tasan wannan k'yauta ba kowa
ke samonta ba sai dan baiwa. Dak'yar ta d'ai-
d'aita ta karasa gidan su. Dan d'uk ji take in bata
dangana da Ummanta ba bazataji sa'ida ba. Ido
cike da hawaye itama Umman ke k'allon Furen,
"Kinga kad'an daga ikon Allah, ki bar kuka haka,
kiyi adu'a, Allah ya inganta miki. Kai Furen ta
k'ada tana goge hawaye a cinyar Umman. "Ki
d'auka wannan tukuici ne ga Allah zuwa ga
hakurin da kikai a jarabawar rayuwarki. Ki d'auka
wannan su zasu zama silar yayewar d'ukkan
kuncin rayuwar ki, nasan kin ari hakuri kin yafa,
Ubangi yai miki albarka Furera... Hawaye ta goge
tana fad'in "Amin Umma. "Umma amma mu
rufeta daga ni sai ke, ko AAA bazai ji ba, in
lokaci yai kowa ya gani, kai Umman ta k'ada, "ai
wannan ba abun fad'a bane Furera, abu ne a
6oye, sai lokaci yayi in sun baiyana a sanar. By
Feenat Ja'afar. 庐NWA. Feenat.my
9/29/16, 2:52 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 44_Koda AAA ya dawo
maganin da aka rubuta mishi kawai ta bada,
sannan ta sanarshi komai "normal". A haka tai ta
rakawa har ta shiga "2nd tremiser", yanzu tana
iya komai,har Abinci ta cigaba da yi ma su Abba.
Iyaka d'ai ita intai ne bazata ci ba sai tuwan
Umma har yau. Sannan t'sawan watannin bayan
ga Aunty Maryam da Ummi da Mama ba wanda
yazo ganin ko lafiya take a gidan. Sai yau da
Aunty A'I tazo dan jin tunda ta dawo a Dubai ba
waya ba zuwa. "Ga nan babyn Maryam har ya
girma tufa. Murmushi tai,kan tace "eh ba,ai
kunsha Dubai, zama ta g'yara, "amma d'uk fa kin
rame Pretty, hope lafiya? Kai ta k'ada mata tana
murmushi, "toh ko d'ai anzo gurin y'ar gida na?
Dariya tai,sai tai kasa da kai, tabbas Aunty A'i
mai Sonta ce, ba tajin zata iya boye mata
wannan. "Allah sa hakan ne pretty,pls ki ban
albishir. Kai ta daga mata tana d'an murmushin
kasa kasa. "Kai,dan Allah ki ban labarin ya y'an
gidan ki sukai da sukaji labari? K'allota tai, "kai
banjin wani ya sani ma bayan mama... Kai Aunty
A'in ta k'ada, "good,kun min d'ai d'ai, g'wara su
gani tashin farko,in yaso sai hawan ruwan mutum
ya hau muga inda zai mutu? Nan suka hau firar
yaushe gamo, yawanci kan matsalar gidan
mazajen nasu ne.. Sosai ta tayata murna har ba
tasan sanda ta ruka musu ba su ma. "Wallahi
Aunty A'i ina son naga kin haihu kema, d'uk da
ina ga kamar... Sai d'ai tai shiru. Murmushi Aunty
A'in tayi, kan tace "kina ga kamar bamu damu ba
koh? Kai ta k'ada, "ba haka ba. Sai ta g'yara
zama. "A da na damu sosai tunda na shekara
hudu, d'uk sosai ban damu wani chan ba,toh
g'wara nima akan maigidan, dan shi kam bai ma
fiya son yara ba, boko ta sha mishi kai da burin
tara kud'i, sam yaran basa a gabanshi. D'uk da
gaskiya ni ban ta6a samun mat'sala a gun dangin
shi ba, sai d'ai na damu daga baya sosai,dan ko
ba komai ina son ganin d'an kaina ko d'aya ne.
Ganin na mat'su ne yasa har da mukai wata
tafiya Umara mukaje muka ga likita, ni kam ban
da mat'sala, sai shi ne suke tunanin a gareshi
take a bangaren "hormones" nashi, wato
(Hormonal imbalance) sannan ga karancin shi
kanshi spm. (Low sperm counts). ''An d'aura shi
a magani, sannan da shawarwari, sai d'ai abin bai
ba. Muna da shekara shida muka sauya kasa
d'uk a dalilin na damun, sai likita ya bada
shawarar ai min "IN VITRO
FERTILIZATION" (IVF) wato a sanya k'wanshi da
nawa bayan "eggs" d'in yai fertilizing. Anyi
nasara, har ciki yakai wata 4 muka dawo gida,
sai d'ai ko wata ba mai ba na samu
"miscarriage". Sau uku ana k'wata haka,sai d'ai
duk basa zama,da haka na hakura na sanya ma
sarautar Allah ido. Sai na ma d'aina damun kaina
da abin,gashi yanzu muna zaman mu lafiya. Sai
dai ko in kad'aicin hakan ya ta6o ni wataran.
Sannan har yau ka'f cikin gidan ban tunanin sun
san haka ba in banda Mama. "Kawo iyanzu da
muke kok'arin cika shekara ashirin da aure.. Kai
Fure ta jinjina, tare da mata fatan alkairi. Bayan
tafi Fure ta zurfafa tunanin rayuwa. Cikinta
watan shi hudu kenan da sati biyu yau, sai yau ta
je gidan su Momy. Kamar kullum chan ta fara
nufa. Su Huwaila wacce ta aure ya mutu ana
parlour. Tun daga kasa har sama ta take
k'allonta. Doguwar Riga ne jikinta da babbar rigar
sanyi fara wacce ta boye asirin cikin. Kau da kai
tai,dan sosai tai k'yau, amma ganin kyashi su
kullum muninta suke gani. "Sannu Huwaila,ina ta
sallama ko baki ji ba? A wukance tace "eh. Sai
tai murmushi. "Ina Momy toh? Harara ta wat'sa
mata kan tace "tana kaina. Ita abin ma sai ya
bata dariya. Har ta juya zata fita sai ga nan
momyn ta fito. Har kasa ta gaida ta, da
mamakinta sai taga tana k'allonta ta amsa. Da ta
dago kai za taga ita momyn ke k'allo. Abincinta
ta mat'sar. Yau d'ai anyi mutunci, dan har ta fita
ba wanda ya tofa mata. Da sauri Momy ta k'alli
Huwaila, "ni fa kamar ciki nake tunanin yarinyar
nan take dashi, kai Huwailan ta k'ada, "haba d'ai
ciki Momy? Wannan katuwar riga kamar tana a
"swisszaland" ba dole ta mayarta mai ciki ba..
Kawai sai ta batar da Momy. Dariya Fure tai,
ganin hakkarta ta cimma ruwa, dan tanajin su
sarai. Dan ba wani sanyin azo muga ake ba a
gari. Mama sosai tai murnar ganinta, bare taga
jika har ya tasa. D'uk sai ta fara sinke kai da jin
kunyar Maman. Momy ke da girki, Abba yai
bangarenta don cin abinci. Wai sam ba tasan zai
dawo da rana ba tunda yau ba weekend ba. Zai
fara balbaleta tace ganan ai na gidan AAA, tuni
ya hau washe baki, "a toh zuba min, sai ku jira
y'ar aiki. D'auka tai suka tafi chan bangaren shi
da k'wandon. Wa'ina ce tasha miyar Egusi da
banda da jan nama. Tuni kamshin ya karad'e
parlourn Abban, shi kam bai jira ba yaje da
kanshi ya wanke hannu. Tuni ya fara kai gara.
Ita kam a kullum mamakin yadda ake ya6on
abincin Fure take,musamman Abba. "Maryam
miyar nan kar ta barki, za kiji haushi.. Sosai sai
had'iyar yawo take, amma isa ta hana ta ci
kamar kullum. Shikam Abba da ya gut'suro sai ya
mika mata, ta d'an y'atsine fuska kamar bata so.
Abba yace "ci d'ai. Daga bata d'aya sai ga
matarka ta t'soma hannu,d'uk loma d'aya sai ta
y'atsine fuska tuni sai gashi har tafi Abban ci.
Sai kam ya hau mata dariya kan ai wannan
"Master Chief ce a cooking. Haka ta d'au
ragowar ta kaima Huwaila, "gashi ku ci, kinga na
sai an wahalar da kai ba,tunda y'ar wahalar ta
kawo. Daga yau mun hutar da rose d'uk
weekend. Tuni k'wa kamar mai jira ta hau ci ita
da ya'yanta. Tun daga ranar su Momy ke cin
abincin Fure y'ar wahala. Sosai ta gama da y'an
gidan k'arfk'af da daddan abincinta. Sai ga nan
Momy na Allah-Allah weekend tayi, sannan
kullum cikin kushe abincin Rose mai aikinta take,
wanda a da gani take tafi d'uk y'an gidan iya
girki. By Feenat Ja'afar. 庐NWA.
Feenat.mywapblog.com
Feenat Jaafar's Mobile Blog
feenat.mywapblog.com
Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 May 2
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 44_Koda AAA ya dawo
maganin da aka rubuta mishi kawai ta bada,
sannan ta sanarshi komai "normal". A haka tai ta
rakawa har ta shiga "2nd tremiser", yanzu tana
iya komai,har Abinci ta cigaba da yi ma su Abba.
Iyaka d'ai ita intai ne bazata ci ba sai tuwan
Umma har yau. Sannan t'sawan watannin bayan
ga Aunty Maryam da Ummi da Mama ba wanda
yazo ganin ko lafiya take a gidan. Sai yau da
Aunty A'I tazo dan jin tunda ta dawo a Dubai ba
waya ba zuwa. "Ga nan babyn Maryam har ya
girma tufa. Murmushi tai,kan tace "eh ba,ai
kunsha Dubai, zama ta g'yara, "amma d'uk fa kin
rame Pretty, hope lafiya? Kai ta k'ada mata tana
murmushi, "toh ko d'ai anzo gurin y'ar gida na?
Dariya tai,sai tai kasa da kai, tabbas Aunty A'i
mai Sonta ce, ba tajin zata iya boye mata
wannan. "Allah sa hakan ne pretty,pls ki ban
albishir. Kai ta daga mata tana d'an murmushin
kasa kasa. "Kai,dan Allah ki ban labarin ya y'an
gidan ki sukai da sukaji labari? K'allota tai, "kai
banjin wani ya sani ma bayan mama... Kai Aunty
A'in ta k'ada, "good,kun min d'ai d'ai, g'wara su
gani tashin farko,in yaso sai hawan ruwan mutum
ya hau muga inda zai mutu? Nan suka hau firar
yaushe gamo, yawanci kan matsalar gidan
mazajen nasu ne.. Sosai ta tayata murna har ba
tasan sanda ta ruka musu ba su ma. "Wallahi
Aunty A'i ina son naga kin haihu kema, d'uk da
ina ga kamar... Sai d'ai tai shiru. Murmushi Aunty
A'in tayi, kan tace "kina ga kamar bamu damu ba
koh? Kai ta k'ada, "ba haka ba. Sai ta g'yara
zama. "A da na damu sosai tunda na shekara
hudu, d'uk sosai ban damu wani chan ba,toh
g'wara nima akan maigidan, dan shi kam bai ma
fiya son yara ba, boko ta sha mishi kai da burin
tara kud'i, sam yaran basa a gabanshi. D'uk da
gaskiya ni ban ta6a samun mat'sala a gun dangin
shi ba, sai d'ai na damu daga baya sosai,dan ko
ba komai ina son ganin d'an kaina ko d'aya ne.
Ganin na mat'su ne yasa har da mukai wata
tafiya Umara mukaje muka ga likita, ni kam ban
da mat'sala, sai shi ne suke tunanin a gareshi
take a bangaren "hormones" nashi, wato
(Hormonal imbalance) sannan ga karancin shi
kanshi spm. (Low sperm counts). ''An d'aura shi
a magani, sannan da shawarwari, sai d'ai abin bai
ba. Muna da shekara shida muka sauya kasa
d'uk a dalilin na damun, sai likita ya bada
shawarar ai min "IN VITRO
FERTILIZATION" (IVF) wato a sanya k'wanshi da
nawa bayan "eggs" d'in yai fertilizing. Anyi
nasara, har ciki yakai wata 4 muka dawo gida,
sai d'ai ko wata ba mai ba na samu
"miscarriage". Sau uku ana k'wata haka,sai d'ai
duk basa zama,da haka na hakura na sanya ma
sarautar Allah ido. Sai na ma d'aina damun kaina
da abin,gashi yanzu muna zaman mu lafiya. Sai
dai ko in kad'aicin hakan ya ta6o ni wataran.
Sannan har yau ka'f cikin gidan ban tunanin sun
san haka ba in banda Mama. "Kawo iyanzu da
muke kok'arin cika shekara ashirin da aure.. Kai
Fure ta jinjina, tare da mata fatan alkairi. Bayan
tafi Fure ta zurfafa tunanin rayuwa. Cikinta
watan shi hudu kenan da sati biyu yau, sai yau ta
je gidan su Momy. Kamar kullum chan ta fara
nufa. Su Huwaila wacce ta aure ya mutu ana
parlour. Tun daga kasa har sama ta take
k'allonta. Doguwar Riga ne jikinta da babbar rigar
sanyi fara wacce ta boye asirin cikin. Kau da kai
tai,dan sosai tai k'yau, amma ganin kyashi su
kullum muninta suke gani. "Sannu Huwaila,ina ta
sallama ko baki ji ba? A wukance tace "eh. Sai
tai murmushi. "Ina Momy toh? Harara ta wat'sa
mata kan tace "tana kaina. Ita abin ma sai ya
bata dariya. Har ta juya zata fita sai ga nan
momyn ta fito. Har kasa ta gaida ta, da
mamakinta sai taga tana k'allonta ta amsa. Da ta
dago kai za taga ita momyn ke k'allo. Abincinta
ta mat'sar. Yau d'ai anyi mutunci, dan har ta fita
ba wanda ya tofa mata. Da sauri Momy ta k'alli
Huwaila, "ni fa kamar ciki nake tunanin yarinyar
nan take dashi, kai Huwailan ta k'ada, "haba d'ai
ciki Momy? Wannan katuwar riga kamar tana a
"swisszaland" ba dole ta mayarta mai ciki ba..
Kawai sai ta batar da Momy. Dariya Fure tai,
ganin hakkarta ta cimma ruwa, dan tanajin su
sarai. Dan ba wani sanyin azo muga ake ba a
gari. Mama sosai tai murnar ganinta, bare taga
jika har ya tasa. D'uk sai ta fara sinke kai da jin
kunyar Maman. Momy ke da girki, Abba yai
bangarenta don cin abinci. Wai sam ba tasan zai
dawo da rana ba tunda yau ba weekend ba. Zai
fara balbaleta tace ganan ai na gidan AAA, tuni
ya hau washe baki, "a toh zuba min, sai ku jira
y'ar aiki. D'auka tai suka tafi chan bangaren shi
da k'wandon. Wa'ina ce tasha miyar Egusi da
banda da jan nama. Tuni kamshin ya karad'e
parlourn Abban, shi kam bai jira ba yaje da
kanshi ya wanke hannu. Tuni ya fara kai gara.
Ita kam a kullum mamakin yadda ake ya6on
abincin Fure take,musamman Abba. "Maryam
miyar nan kar ta barki, za kiji haushi.. Sosai sai
had'iyar yawo take, amma isa ta hana ta ci
kamar kullum. Shikam Abba da ya gut'suro sai ya
mika mata, ta d'an y'atsine fuska kamar bata so.
Abba yace "ci d'ai. Daga bata d'aya sai ga
matarka ta t'soma hannu,d'uk loma d'aya sai ta
y'atsine fuska tuni sai gashi har tafi Abban ci.
Sai kam ya hau mata dariya kan ai wannan
"Master Chief ce a cooking. Haka ta d'au
ragowar ta kaima Huwaila, "gashi ku ci, kinga na
sai an wahalar da kai ba,tunda y'ar wahalar ta
kawo. Daga yau mun hutar da rose d'uk
weekend. Tuni k'wa kamar mai jira ta hau ci ita
da ya'yanta. Tun daga ranar su Momy ke cin
abincin Fure y'ar wahala. Sosai ta gama da y'an
gidan k'arfk'af da daddan abincinta. Sai ga nan
Momy na Allah-Allah weekend tayi, sannan
kullum cikin kushe abincin Rose mai aikinta take,
wanda a da gani take tafi d'uk y'an gidan iya
girki. By Feenat Ja'afar. 庐NWA.
9/29/16, 2:53 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 46_"Hand golf " ya sa
dan duba "CM" da mamaki ya k'allota, sai d'an
nishi take tana zufa,sosai yai mamaki,da sauri ya
fasa ruwan, ganin yaki, Waje yai gun AAAn, ina
zaton zata iya, InshaAllah,kuyi mata adu'a kawai.
Kai ya k'ada, "za mu iya shiga? Kai ya k'ada
shima likitan, "sosai, musamman kai, za ta fi
bukatar ka kusa. Maryam ya je bama abin
g'wajin da doctorn ya bashi,tuni ta sanar da
Umma da dasu Aisha. Tashi Umman tai kawai ta
shiga bayi ta d'auro alwala. Tara da wani abin,sai
ta zauna sallaya tana mai rokama y'ar tata sauki
da Nabiyur Rahmati. Komawar likita har Nurse
tai gunta, ganin yadda take ta ko'k'arin nishin
fitar D'a. Gaskiya likita yana jinjina mata,ganin
yadda ta dage sai ta haihu da kanta. Kawai sai
ya hau had'a abubuwan taimakon labor. Tana
t'saka da nishi sai ga nan AAA shida Maryam,
nurse tace ya shiga man ganin ya t'saye kawai
k'allon Furin yadda take nishi gumi na zuba
tamkar wacce ta had'iyi kunama. Kai ta daga
kamar ance k'alli kofa,suna had'a ido kamar zai
sau mata kuka.. Ido ta rufe,cikin masifa tace
"Fita.. Ka fita bana son ganin ka... Da sauri likita
da su Maryam suka jiyo,ganin AAAn ne sai abin
ya basu mamaki, cikin rawar murya AAAn yace
"Pretty ni ne fa... Da sauri ta bud'e ido, kawai sai
taji mugun haushi, "eh kai d'in.. Baki sake yake
k'allonta.. Ganin yaki fita ta juyo gefe, k'walin
"hand gulf'' ta d'au ta hulo mishi, cikin balbalin
masifa ta rufe ido tana sai ya fita... "Ya fita
kawai... Kawai sai ta farke da kuka... Cikin rawar
murya yace "yi hakuri, na fita, sannu, kiyi hakuri,
Allah sarki AAA. D'uk sai ya basu tausayi. Yana
fita ya goge k'walla, tabbas yasan ba karamin
wuya prettyn shi ke ci ba, tunda har zata iya
t'sanar ganinshi. Da sauri ya d'au waya yana
kiran Mama. "Ka k'wantar da hankalin ka,Muh'd
ya sanar ni, zata haihu lafiya.. Ka d'aure. Dak'yar
Maman ta d'ai d'ai ta shi. Sai d'ai Furi har goma
shiru ana ta fama. Tuni Maryam har ta fara
kuka. Abba karan nan ta kira, shima tuni ya taho
gida d'uk sai ya ji kamar bazai iya ci gaba da aiki
ba. Jin Maryam na kuka yasa ya d'au jarka ya
hau karanta mata d'uk wata adu'a ta saukin
haihuwa, "Umman su ko d'ai zaki je ne? Kai ta
k'ada, "bana tunani, sai ta share k'walla. "Sai d'ai
nasan d'uk inda Furera ta t'saya tana jin jiki..
Ganin tana hawaye yasa yai mamaki. "D'uk
yaran nan sun haihu lafiya Umman su, itama zata
haihu,in d'ai har tasha wannan adu'ar da yardar
Allah. Kai ta k'ada, "Allah yasa, amma haihuwar
Fure ba irin tasu bace... Komai ta sanar ma
Abban, nan yai ta mamaki, sai ya fita makotan
su, ak'wai dabino,ya samo danye fresh wanda
aka jijjige a take mai bauri. Yasa Umman dakeshi
cikin sauri, su basu rabo da zam-zam y'an Naira
dari, dashi ya had'a da ruwan tofin, ana haka Ada
ta shigo ajiye yara zata asibiti harda breakfast
d'in ta. Nan Abba ya bata sako, tare da ce mata
ta tabbatar tasha. G'wag'war maya ake da Fure
da likita kan bazata iya ba tana musun zata iya,
adu'a ce kawai fal bak'inta. Babu wanda ke a
K'wak'walwar ta sai Allah. Lokacin zuwan Ada
har Ummi ma tazo,tana zaune kusa da yayanta
wanda yake ta sallar "Dhuha" baji ba gani, in ya
hau "Sujjada" yakan jima yana rokar ma prettyn
shi sauki gurin Allah. Maryam ta kira, sai gata
tazo,idon nan ya k'ada, "Maryam ya akai? Kai ta
k'ada, "ina zaton ba D'a d'aya ne ga Ya Furera
ba, dan naji tun dazu likita na ambata mata
"Babies" kan bazata iya ba ita kad'ai. "Ba
komai,kiyi ko'k'arin ki bata wannan inji
Abba,InshaAllah zata iya tunda ansa Allah. Kai ta
k'ada, kan ta k'ar6a tai ciki. Sai d'ai fur likita
yace zata t'sayar mata da labor wai ya koma
baya,tace adu'a ce. "Zansha Doctor, adu'a ce, a
bani dan Allah.. Kai ya k'ada, dan shi yanzu
komai aka ce Allah kawai yinshi yake,dan yaga
Aya.... Cikin Rahmar Ubangi, ko minti goma batai
da sha ba taji wani nishi ya taho mata, da sauri
likita ya k'alleta kan ya d'akko abin ka'ri yai
mata. Baki Maryam ta toshe,take ta k'alli robar
dake a hannunta. Da ikon Allah ya zaro baby,sai
ga nan wani na biyo bayan d'aya. Tuni Furen tai
baya tana mai jan numfashi sama. Da gudu
maryam tai waje tana murnar taga yara biyu.
"Yaya Ahmad!..Ya Ahmad, yana d'urkushe yai
sujjada kusan minti biyu adu'a kawai yake ma
Fure. Ganin haka ta ruko hannun Ummi da Ada,
"wallahi twins ne, ta haihu naga... ''Assalamu
Alaikum warahtullah... Yai k'waya d'aya hagu da
dama. Cikin azama yace "Pretty fa? Sai ta zuba
mishi ido, dan sam ita bata ma kula da halin da
take ciki ba. Ganin ta zuba mishi ido yasa da
sauri yai hanyar kofar room d'in. Samu yayi likita
na fad'in zaki iya,ki kara nishi tana k'ada kai,
gaba d'aya numfashin ta sama yake. Ganan yana
ganin wani abu bak'i-bak'i likita na ko'k'arin fitar
shi. Da gudu yai kanta tare da kiranta, dusu-dusu
ta fara gani, tuni ta hau yunkuri kamar zatai
amai, da sauri likita ya jawo babyn da Allah ya
kara tunkudoshi. "Sir... Da sauri Nurse ta fara
nuna mishi Furen dake ko'k'arin d'auke numfashi
Ahmad na jijjiga ta. Cikin sauri ya bama d'ayar
Nurse d'in babyn kan yace "oh no! Cikin zafin
nama ya jona mata "Oxygen", tuni ta fara sama
da kirji tana jan numfashi, ko dusu-dusu ta d'aina
gani, cikin sauri ya zuke wata allura bai wata
wata ba ya chuka ta jikin cinyar Fure. Numfashi
mai k'arfi taja,wanda yai d'ai-d'ai da k'wala kiran
da AAA yai mata "PRETTY.......................... By
Feenat Ja'afar. 庐NWA. Feenat.mywa
9/29/16, 2:55 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 47_Ina Pretty ta lula,
Kanta yazo yana d'anna mata kirji yana k'allon
numfashin, sai d'ai ita ko gizau, tuni Ahmad ya
kafawa hannun likita ido ba ko kiftawa, ya ma
kasa kok'arin hanashi ko sashi,hawaye kawai ke
zubar masa, da sauri likita yace nurse ta nemo
mishi likita guda biyu,ya sanarta sunan su,kan su
zo ya kara mata wata allurar, ganin ba nasara
yasa Ahmad kawai ya zame gun yana kuka
kamar yaro, shi kenan shi, ya zama maraya. Kai
da g'wiwa ya hada yana rusar kuka, yayinda likita
yake ta aikin shi. Su Maryam da suka leko tuni
sukai waje suka had'a kai suna kukan Fure,dan
d'uk sun saddakar ta ma mutu. Wani numfashi
Fure taja mai k'arfi, a hankali ta fara mutsu-
mutsu d'ai-d'ai shigowar likita d'aya.
"Pharmacy".. Cikin murna likita ya kira shi, da
sauri ya daga jin tarin Furen,sai d'ayan likitan ya
cire mata Oxygen d'in. Da gudunshi ya karaso
yana kiranta, cikin hankali ta fara bud'e ido,komai
ya fara dawo mata. Akan AAA ta dire,wanda har
yanzun hawaye yake rike da hannunta a bak'inshi
yana d'an dariyar murna tare da shafa gashin
kanta, sai d'ai koh sannu ya kasa furta mata,a
hankali ya d'aura kanshi a kirjinta kamar wani
yaro. Cikin hankali ta d'aura hannunta a kanshi
tana hawaye da sigar lallashi, tasan da ta mutu,
da AAA shi zai fi kowa shiga a wani hali. Da
taimakon manyan likitocin suka had'u suka
temaki matar "pharmacy". Tuni su kuma Nurses
suna chan a d'akin taimakama yaran. Sai da
d'aya Nurse ta fita tace ma su Maryam toh su
d'aina kuka karamin suma tai... Sai da ya
tabbatar ta g'yaru da komai sannan yahau musu
godiya. Har aka gara ta d'akin hutu na
musamman suna a manne da hannun juna. Tuni
kuma aka hau buge-buge su Ada su su Ummi kan
Fure ta haifi y'an biyu, shikam suna a gado
d'aya. Sai ga nan yaran su an garo musu cikin
gadon yara. Wani ihu su Maryam suka buga da
suka ga uku, tamkar yara harda dan t'sallen
su,tuni suka bi Nurses d'in d'akin da Fure take
suna murna, kam suka ce musu banda hayaniya,
amma sun san ai ba abu ne mai wuya ba. Wai sai
a sannan ya ma tuna da yaran, tuni kowa ya d'au
d'aya, ummi tace "woow.. Adama tace "k'yau...
Yayinda Maryam tace "MashaAllah, kawai sai
nurses d'in suka sa dariya, dan ko su suna ta
yaba kyaun yaran, gasu da dan girman su, kan
suka had'a baki gun fad'in "Congratulations sir"
kai ya k'ada musu, kan yace "yau ak'wai k'yautar
magani a store. Na hannun Maryam suka ce
"wannan ne Hassan, ga nan Hussain, na hannun
Ummi kuma itace mace "Gambon su, kan suka
fita. Wajen gadon su Fure sukai da yaran, harara
ya kai musu cikin wasa, "ai munyi fad'a dasu,
kad'an ya rage na rasa Momman su ya k'wanto
kan Furen suna musu dariya har Furen, a hankali
ta lallashe shi kamar gaske. Ido kawai suka zuba
ma yaran da suka d'aura musu su. A hankali ya
k'allo Furiin, tambayarta yake shin tasan dasu?
Kai ta ka'rkace mishi tai kallar tausayi, ido kawai
ya zuba mata, Furii ta mishi komai.. Ga ta bashi
yara masu kamar shi, sai sumar(gashi)Furiin da
suka d'akko da d'an bak'in nan. Kan kace wani
abu sai ga nan y'an uwa sun fara diddikowa,
harda Mama ta wanke ido tazo ganin twins, sai
d'ai suna ganin uku sai su hau kabbara. Abba
cikin sauri yai d'akin Momy da har yanzu d'aya
saura bata bud'e d'aki ba tana bacci,wanda a
zahiri in ta dad'e takai goma,amma ranar Allah
ya k'wantar ta. Mut'seke ido take ta bud'e, ganin
Abban sai wage baki yake yasa tace "Alhaji
lafiya? Cike da murna yace "Maryam matar
Babana ce fa ta haifi y'an uku.. Cikin rashin
fahimta tace "waye hakan? Sai ta kai hannu kan
dank'wali tana warewa, "a wanake dashi bayan
Ahmad, Furera ce ta haifa ai..... Hannu kame a
kai Momy tai poster, jin Bud'e kofar gefe yasa ya
juya cikin murna, Huwaila ce, "Abba wa nake ji
kana haihu? Cikin murna yace "Sa'a matar
Ahmad, uku fa,ras, kuma da kanta... Waya aka
mishi sai yace "bari ga nan Ummi. Cikin zakuwa
yai waje yana amsa waya, baki sake suka bishi
da k'allo, Momy na furta "Furera kuma?... Cikin
kok'wanto. By Feenat Ja'afar. Feenat.mywapblo
9/29/16, 2:58 AM - Queen Safiyyert馃憫: [5/4, 10:09 PM] Feenat Ja'afar.: "JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
48_"Kai Momy ina fa Abba bai ji da k'yau bane,
wane irin Haihuwa? Kuma y'an uku?.. Kai
"impossible".. K'allonta kawai Momy take, "tun
ba yau ba na fuskanci yarinyar nan tana da
ciki,amma fir kika karyata.. " no ba ma wannan
ba, saboda rashin mutuncin ya mot'sa musu,kinji
wai har akaita asibiti Ummi taje bamu sani ba?...
Tuni ta hau kumfar baki, kan zasu ga ba inda
zata toh.
"Wallahi Momy kar kije, tunda an nuna baki isa
ba kawai. Tuni ta hau zigata, kuma wai sai ta
hau buga ma su Rukayya da Aunty Jidda waya,
kowa ya ji sai ya na nata haihuwa kuma? Y'an
uku?.
Kamar k'wa yadda Momy tace d'in kin zuwa tai,
sai Huwaila ce taje ta ga k'wak'waf.
K'wanan su biyu yasa a sallame su, tare da
d'aukar Nurse mai zuwa duban su, dan sosai
jama'a sukai yawa.. Tun a asibiti Fure tasan tai
haihuwa, dan Abba mota biyu sukai zuwa ganin
yara shida Abokanshi, kowa yazo sai ya direma
Fure y'an banki.
A gidan ma haka, jama'a sosai, kusan kullum
Aunty A'i na nan gidan kusa da yara, Fatee na
jan nata tsohon cikin, shi yasa d'uk tai lum,
amma d'uk da haka tana a hanya kullum,
Hassana an zo, dak'yar aka d'anne zuciya ganin
ikon Allah, sam AAA baida k'arya, amma akan
yaran shi ya tada ta, d'uk wani kaya na ban
sha'awa yara sun sha su, an k'awata d'akin su
g'wanin ban sha'awa.
Yara sunci Hassain,Hussein, da Hasna(pretty),t
uni tun a asibiti yai ma yaranshi huduba, sam ba
sunan kowa, dan kowa yazo yana son mai suna,
Hasna kam wai ta mishi k'yau, shi yasa ya sa
mata shi, dan ta chanchanci zama pretty 2 wai.
Har sukai k'wana 5 ba Momy ba Aunty Jidda bare
Rukayya, d'uk rashin shiga jama'a na kishiyar
Rukayya amma tazo gidan Fure a karo na farko.
"Anya mutanan nan zasu ga Annabi Ya Furera?
Ace tunda haihu, ba wacce ta leko dubaki cikin
Momy da Aunty Babba? Murmushi tai kan ta
k'alli Maryam d'in, "mey kike so toh nace? Tunda
kinsan yadda nake gunsu.. Baki ta ta6e Maryam
d'in, Aisha tace "ki barsu ke d'ai Fure, kar ki fara
komai, aciki har hudubar hanasu su Hasna da
ake miki..
Murmushi tai ta k'ada kai, ita kad'ai tasan mey
zatai.
"Ba wanda zan hana yara,asalima nai alkawarin
d'uk wacce ba tazo ba zan kai mata har gida ta
goya.
Karamin t'saki Maryam tai, "wallahi ba mahalukin
da ya isa na haihu bai min barka ba na kai mishi
D'a, wallahi ko zai mutu. Tab, karshen kyyaya
kenan wannan... Shiru tai lokacin da Aisha ke
zungurarta, su Momy ne t'saye bak'in kofa ita da
su Aunty Jidda.
"Momy shi yasa nace miki bazan zo gidan nan
ba kika tilasa min, sam na ki jinin had'uwata da
shegiyar yarinyar nan.. Ta nuno Maryam.
Ciki momyn ta shigo, tana mai harar kowa na
parlourn, kasa Fure ta s'akko cikin girmamawa,
ita kam Maryam baki ta ta6e, tare da dan
gunguni ciki ciki.
"In bata nuna haka ba ina za kusan y'ar gidan
mai waldar mashin ce ita... Da sauri Fure ta
dago, Rukayya ce, tuni taji zuciyarta na tafasa,
ga nan Huwaila, ga Aunty Jidda, ga kuma Momy.
Wani murmushi tai, kan a hankali ta girgiza kai,
Lalle Allah a yau ya ara mata ranar da ta jima
tana neman zuwanta, ranar da har sallar t'sakar
dare tai dan zuwanta.
"Mtsww.. "Alhamdulillah, a ko ina zan bugi kirji
sannan nai alfari, "of course, ita ce sana'ar uban
mu, amma kamun nan sai ki fad'an sana'ar taki
uban...
"Maryam... Cikin t'sawa Fure ta kat'seta, "ki
kama kanki, baki ta ta6e, Cikin fusata Rukayya ta
mike, ''karya na fad'a, iyalan t'siya da t'siya, an
zo aci aziki ai dole a haiho y'an uku, kinga ko ba
komai an mamaye gida.
Ido Maryam ta rint'se, a rufen tace "Ya Fure ba
miyi dake zaki t'sayar ni a batun nan ba fa,
saboda haka wallahi sai na furta.
Ido ta bud'e, har da mat'sowa kusan Rukky, su
Momy da Aunty Jidda ido ne kawai nasu, dan
sosai sun yi mamakin fitsare idon Maryam, wai a
gaban su take wannan rashin mutuncin?
"Sana'a ba chacha bace, ba kuma satar kud'i
bace a Ak'watin gwamnati, a jerin barayin
g'wamnati dole uban ki ya fito ciki, ga chacha
kamar ibada, ga neman mata kamar d'an taure,
ga....
Mari Fure ta sakar mata, cikin t'sabar fusata ta
fara mata fad'a, "wa ya fad'a miki wannan abin?
Rike da kunci Maryam tace "sana'ar ubanta na
fad'a, ko ke ba k'ya kishin naki uban?....
"A'a ki barta, ki barta ta kai Aya, tanan zamu san
lalle an gaji t'siya da talauci, bak'in ciki take da
dukiyar uba na, kuma wallahi yafi Ubanku Malam
Muhamm...
"Rukayya....cikin t'sawa Fure ta kat'seta, kan ta
nuno ta da hannun cikin t'sananin fushi da
"ki iya bak'in ki, ya zama ranar karshe da zaki
kara wannan kuskuran na ambatan sunan
mahaifin mu ciki. Kiyi komai, amma wallahi ki
t'sallake wannan, ba zan d'auka ba... Ta karasa
tana mai kawar da kai gefe,
Ba wanda ba k'alleta ba lokacin da tai t'sawar,
yayinda su Ahmad suka karaso bak'in kofar
parlourn suka t'saya gefe.
Harara Aunty Jidda ta k'wada mata, "dallah rufe
mana baki a gun, ji ta, har wani abin tunkaho ne
ga alfari ga d'an waldar, an fad'a muku ya'yan
mai walda, matsiyata kawai... Ido Fure ta rint'se,
kan ta dago ido ta sauke su kan Aunty Jidda.
"A fad'an komai, amma uban mu daraja ne
gareshi matuka a gun mu, a gaskiya yau hakurina
zai kare akan hakan, kai ta girgiza, "dan Allah
sam bazan d'auka ba, sam Allah.
Sai ta sa bayan hannunta ta goge y'ar k'wallar
da zata ta fad'o mata.
"Momy kina jinsu ba kiyi magana ba? Sunci sun
koshi wai har ita wannan tana da baki? Yaushe
kika samu y'ancin kai dan kin tashi a JUYA?
Shine har zaki wani hau fallin fararo budurci
bayan haihuwa?... Cikin sauri Maryam tace
"Dallah rufe mana baki, ki bari y'an gidan masu
y'ancin magana suyi, dan yanzu sunan JUYA ya
koma naki... Tunda gado ta zame muku sai ki
haiho...
Kanta suka yiwo ita da Huwaila, tuni Maryam
taci damara,Fure na ganin haka ta shiga t'sakiya,
yayin da Ahmad suke kuts'o kai dan jin abin na
yawa,
"d'uk wanda ya ta6a ta wallahi zan zage muci
uwa a gidan nan dashi... Ido ta rufe tare da
sauya musu kama "hakuri ba hauka ne ba, kar ku
kaini bango Wallahi.
"Kuma ki sani haihuwar ba gado bace, dan da
tuni yaya Babba(Aunty Jidda) ta gada, ba gado
bace, wallahi da tuni nima na gada, ba gado
bace, dan da tuni kowa a duniya ya gadeta, dan
ba dan uban da aka ta6a ruwan shi daga sama
ya fad'o, kowa uwa ce t haiho Shi a duniya.
By
Feenat Ja'afar.
[5/4, 11:53 PM] Feenat Ja'afar.: "JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
49_ If you feel so high? Then Stay away.. Or
else.. K'yam suka t'saya, baki sake suke k'allon
Fure tai turanci,
"Wa? Da wacce ta isa ta dake ni ne ina k'allo? Ai
wallahi da mutum ya debi hakoranshi a kasa, na
rantse.
"Toh ba anan ba, sai d'ai ku tafi gidan uban ku
yau, ku tattare ku kara mai, aje inda aka fi
k'wari.
Baki Maryam ta ta6e tana since damara, yayinda
da Fure ta rint'se ido.
"A gaskiya bazan iya fita ba izinin mijina ba, kiyi
hakuri Aunty Jidda... Cikin fusata ta tashi tana
huci,
"Are you challenging me?.. Murmushi Furen tai,
kan ta girgiza kai,
"No,am not, sai Aunty Jiddan tai murmushin
mugunta, sai dai kan tai magana Fure ta karasa
da "Amma "If it comes to that... Sai ta juya
bayanta tare da rint'se ido.
"Then i challenge you"....
Su kam su Ahmad jin abin na yawa yasa sukai
cikin parlourn.
Aunty Jidda tace
"Eyeee... Lalle kin koshi Fure... Uban waye
gatanku a garin nan? Da sauri tace "Allah, da
kuma...
Marin da Momy ta sau mata mai mot'si ne yasa
ta kasa karasa wa tare da yin baya zata fad'i taji
an rukota da Hannu da yawa.
Sanye yake cikin farar "suite" da "purple" d'in
y'ar ciki, sosai yai k'yau, da ganinshi Naira ta
zauna mishi, ganan fatar nan tai k'yau... "Ya
Suleiman, cikata Ahmad d'in yai,dan Ya Suleiman
yafi rukota, da gudu maryam ma tai yo wajen shi,
kwai sai suka ruk'unk'umeshi tare da sakar mishi
kuka. Hannu yasa d'uk ya zagaye kafad'un su,
har wani ka'rkarwa jikinshi yake,tuni ran y'an
maza ya tashi.
Cikin Azama zai gun Momy Fure ta rike shi, kai
take girgiza mishi hawaye na zuba,ganan kukan
dan Maryam ya karad'e parlourn, kawai sai ya
rint'se ido, tare da cije le6e.
"Muje, kan na aikata kuskure Maryam, Furera
d'akko shiga ki fito. Kai ta sunkuyar, kan ta dago
su kan Ahmad, wanda idonshi rintse bazaka gane
halin da yake ciki ba.
"Ahmad, ka ban izinin fita dan Allah.
Ido a rint'sen yace "ki bi umarnin su Momy, ki je
gida Furera, kije...
Kawai ya juya ya fice a parlourn cikin sauri.
Ido ta rint'se, wato taje? Kawai sai ta k'ada kai.
"Sai ai gaba ya sallama ki, Huwaila tace "kuma a
bar mana yara.. Harara Maryam ta sakar mata,
"ko baku fad'a ba, dan mu kad'ai aka kawo
mu,babu su cikin garar auran mu.
"Ku barsu Fure,ku saman a mota. Wajen Hasna
Fure tai, tana a k'wance ta fara ko'k'arin goyata
Rukayya tazo, "bakiji ki bar mana yara ba aka
ce? Tana jin tana ko'k'arin d'auke ta ta dago a
tunzure ta sau mata mari, "uwar kice tai min
nakudar da zan bar muku yara na? Eh? Toh naga
wanda zai t'sayarni in ya haifu.
Jan Rukayyan Aunty Jidda tai, "ku k'yale su suje,
mey za kici da yaran bare a huce a kanki?
Ko ta kansu basu kara yi ba su Ada sukai waje
da sauran, fure ta d'akko hijab, yayinda d'an
gidan Maryam ke t'sala kukan ta d'auke shi,
t'sawa ta daka mishi, "ai ba inda zaka bini
yaro,tuni ta yakice shi tai waje,kasa yai yana
bori da kara jiniyar kukan shi.
A bak'in gate Fure ta dago tana k'allon Ahmad
dake cikin motarshi a k'ulle, da sauri ta d'auke
kai ganin zai k'allota ta shige mota.
By
Feenat Ja'afar.
庐NWA.
9/29/16, 2:59 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 50_Suna ko'k'arin jan
mota sai ga nan Muh'd yai sauri fita a tashi yazo,
t'sayawa ya Suleiman yai tare da K'awar da
kanshi, tuni Maryam ta k'ank'ance ido, kofar ya
bud'e, "Ya Suleiman ka'r kai haka, "Maryam ka'r
ki tafi, dan Allah Aunty Furera kuyi hakuri, yanzu
AAA ya kira ni, mey yai zafi haka?... "Ka shiga
daga ciki zasu kora maka bayani, sannan tafiya
kam nayi na gama, wallahi ka ma biyo ni da
takkadda ta.. Murfin motar ta ja, tuni Fure ta sau
kuka lokacin da Ya Suleiman ya ja mota, shi kam
Muh'd ya ma kasa komai. Da sauri ya juya jin an
dafa kafad'arshi, AAA ne idonshi yai jajir, "ka
shiga ka d'akko yaron ka ciki yana kuka, ka'r ka
kula kowa,kawai ka fito mu tafi, kai ya k'ada
mishi. Rukayya ya samu tana k'wadawa Abulkair
t'sawa... "Dallah yi mana shiru agun... "Tunda ta
barka kowa ma ba mai d'auka, irin t'siya da
talauc.... Tass, da sauri suka jiyo,wanda ba shiru
Rukayya ta dafe gun mari a ka'ro na biyu yau,
tuni Abulkhair yai shiru. Ilahirin Parlourn sun
zuba mishi ido, sam shi baida fad'a, asalima shi
mai bark'wanci ne, sam zai wahala kaga bacin
ranshi, tuni sai ya sauya musu kama. "Ashe
rashin mutuncin ki ya kai haka? D'an nawa ne
gadon t'siya? "Muh'd, mey nake gani? Matar
Yayan naka ka mara?... "Ta Allah Aunty Jidda da
mari ne kawai, da wallahi sai nai kasa kasa da
ita a gidan nan.. Charaf Huwaila ta chafe, "Aunty
Jiddan? Cikin fusata yau yo kanta, da sauri ta
nufi bayan Momy, kawai sai ya sunkuci d'anshi
yai hanyar Parlour, "Yau na tabbatar Mama Uwa
ce Momy, kuma Maryam kamar ta dawo ta gama,
dan ba mai raba min aure ban shirya ba. Zaune
suke ya Suleiman na t'sara ma su Umma da
Abba abinda ya je ya tarar, "G'wara da bakai
hukunci ba Sule, Allah ya muku albarka, ki bar
kuka uwata, d'uk na halili mai kishin iyaye ne,
tabbas anzo gabar da bazan hana ku k'ar6ar
y'ancinku ba, kuyi hakuri, Allah ya raya muku
yaran ku,kema Maryam banso kin bar musu
yaron ba sam, bari na koma gun aiki, ku kara
hakuri. A gado Umma ta k'wantar da Hasna,kan
ta d'akko Hussein da Hassein dake parlour. A
hankali Fure ta zame kusan Hasna ta
k'wanta,d'uk idonta yai mata nauyi dan kuka,
k'allon yaran kawai take hawaye na zubar mata.
A hankali ta kai hannun kan sumar kan Hasna.
K'allonta Umma tai cikin tausayin y'artata, tana
fatan wannan ya kasance cikin karshen kuncin
rayuwar ta. A gefe Maryam ta zauna. "Kuka
bazai miki magani ba Fure, kar kisa damuwar su
har ta ja miki mat'sala, kinga kina da d'anyan
jego, Allah zai bi ku hakkin ku ne kuna zaune..
Kai Maryam ta k'ada, "Allah Umma na hakura da
auren nan, wallahi har Muh'd na t'sani ganinshi
balle danginsu... Hawaye ta goge a karo na farko
tun faruwar abin. Shiru Umman tai, tasan yanzun
d'uk suna a cikin fushi ne, sai ta tashi ta basu
waje tare da nufar kitchen dan d'aura ma Fure
ruwa. A gaban Mama suke bayan sun t'sara
mata abin da ya faru, dak'yar Ummi ta goya
Abulkair sukai waje don rarrashi, tamkar yaro
haka AAA ya d'aura kanshi kan kafar Mama yana
hawaye bayan ya gama t'sara mata. Shikam
Muh'd yana a gefe sai fad'in Allah kawo Abba
yake. T'sam Mama tai,tabbas lokaci ya yi da
zata takawa Momy birgi, ko Abba bai d'au mataki
ba a wannan karan zata t'serar da mutuncin
sirikanta, dole su zamto y'antattu cikin gidan
nan.. Dole ne wannan. By Feenat Ja'afar.
Assalam Alaikum warahtullah.. Ku diba wannan,
sannan ai min affuwa, zan d'an yi tafiya,Kila ku
jini inna samu time... In anji chilu toh sai na
dawo... Luv you.
Like 路 5 路 Reply 路 Report 路 Ma
9/29/16, 3:00 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 51_Dawowar su kenan
sukai bangaren Mama, Muh'd na ganinsu ya mike
yai waje,yayin da AAA yai saurin goge
idonshi,kan ya d'aura bayan Muh'd, da k'allo
Momyn ta bishi, bata ta6a ganin AAA cikin
yanayin nan, sannan koh sannu da zuwa bai mata
ba,asalima ko inda take bai k'alla ba, ita kam
Mama kai ta kawar,da hannu Momy tai ma su
Aunty Jidda suje bangarenta. Kamar kullum ta
fara zazzage ma Mama kan wai Muh'd ya mata
rashin kunya akan Matan su marasa mutunci...
Sai balbali take,"in na zartar toh ta zaunu gidan
nan, basu ba dawo mana sai sun san mutuncin
mu tukun... Murmushi Mama tai,kan ta k'allota a
ka'ro na farko tun t'sawan shekarun su kuma ta
tanka. "Hajiya Maryam wane mutuncinku ne yai
saura gunsu da gaba kike tunanin ya karu? Iya
kok'ari yaran nan suna miki biyayya ka'r ma
Matar Ahmad taji bayani, wanda nai imani koh
manyan sirikan gidan nan basa miki, haihuwa tai
har t'sawan k'wana biyar kan kukaje ganinta,
d'uk ke ya kamata ace kin fara zuwa ganinta ko
dan irin gorin da kuke mata dan bata haihu,
bazan boye miki ba, a gaskiya banjin sam dad'in
irin abinda Furera ke fuskanta a gunku sam...
Cikin mamaki ta k'allo Maman,kan cikin fusata da
isarta ta t'sayarta,tuni suka fara kace na
ce,sabon lamari,wanda sam ba halinsu ba. "Sam
ya isa ikon,dole a barsu su wala kamar d'uk
sauran sirikan gidan nan.. Safiya tunda kina
neman ja dani,toh naga wanda zai dawo mana
dasu gidan nan, yara ni nake iko dasu ba ke ba,
dan ni naci fitsarin su da kashinsu, dan haka ba
mai nuna min isa kansu... "Hajiya Maryam kamar
sun dawo sun gama ne, kuma kisa ido.. A fusace
momyn ta tashi, "wa ya isa dawo dasu gidan?
T'saye itama Maman ta tashi, "ni Safiya da kaina
zan dawo da sirikaina gidan nan, karan nan kin
kai ni karshe kiyi hakuri... ''Safiya sam,kar ki ma
fara, ki bar Maryam tai son ranta... Abba da
Muh'd da AAA ne t'saye bak'in parlourn.
Murmushi momyn tai ma Mama lokacin da su
Abban ke karasowa, ita kam Mama kai tai kasa
dashi,tasan Momy ita ke da fad'a aji ko agun
Abban su AAA, amma dole karan nan ta nuna
itama mai iko ce, sai d'ai da mamakinta taji Abba
na fad'in, "Wanda yace su tafi shi zai dawo dasu,
Maryam da kafarki nake son ki dawo da yaran
nan d'akin su... Cikin mamaki suka k'alleshi,
barin Momy da ta cika da mamakin Abban,Muh'd
harda g'yada kai da murmushi. "Sam banga aibun
yarinyar nan ba Furera, tana kula damu,gata da
kok'ari, amma tun ba yau ba nake mamakin
yadda jininta bai gamu da naku ba. "Sosai zan
bata ran d'uk wanda zai fara tarwatsa gidan
ya'yana, ina umartarki da kije tun muna sheda
juna ki dawo da yaran nan, Tashi yai kamin ya
k'allo Momy, "kinji na fad'a miki...ya k'arkade
rigarshi da bambami ya fita,yana mai kara sanar
da Momy zancen shi. Da d'an harara ta k'allo su
Mama, "Allah ya kiyashe ni biko wallahi, yau
naga t'sant'sar butulcinki Safiya, kuma in nice ba
ni ba yaran ki, ka'r in kara ganin keyar wani
sashe na.. D'uk ki jijasu na bar miki... A fusace
tai hanyar fita AAA yai saurin binta, "Momy abin
bai kai haka ba pls.. A fusace tace "ka'r na kara
ji ka kirani da Momy, ban haifeku ba, da harara
tabi mama kan tai waje, binta zai kara yana
k'allon Mama, kai ta k'ada mishi, hakuri ta basu
kan sui hakuri, sannan ka'r su kuskura fara yi ma
Momy rashin kunya kan Matan su, su bar komai
hannunta, sannan in ta huce su lallasota,kai suka
k'ada mata. Huci take tamkar asman ta zata
tashi, da sauri sukai kanta, "Momy lafiya? Hannu
take kaiwa baki,da sauri Huwaila ta d'akko mata
ruwa ta bata,zuwa chan ta nutsu. "Yau Alhaji ya
nunan karshe na,yai min tozarci... nan ta
k'washe yadda sukai da Abban ta sanarsu, tuni
suka hau zigata kan ka'r taje ko'ina, su d'in wa??
~~~~~~~~~~~~~~~ "Allah takaddarmu zaku
bamu, ka sanar da ya Ahmad ma tun wuri...
K'allon Maryam d'in Furen kawai take yadda ta
rufe ido tana y'arfawa Muh'd masifa cikin
waya,Kai ta k'ada, ina ma zata iya yiwa AAA
haka ko taji saukin zugin zuciyarta? kawai sai ga
nan hawaye ya zubo mata,bayan hannunta tasa
ta goge, tun jiya AAA yake aiko text amma ta
kasa ma k'allon wayar bare ta d'auka ta gani.
kamar had'in baki kuwa Maryam na gama waya
sai ga nan call na AAA akaran farko tun jiya.
Sautin "Ringtone" nashi na ("nothing gonna
change my love 4 u") ne yasa ta k'alli
wayar,maimakon taji sanyi kamar kullum in AAA
na mata baitin koh kidan na tashi kawai sai taji
wani haushi da t'sanar wakar ya rufe ta. Cikin
zafin nama da masifa ta d'au wayar ta seta
bango da niyar k'wad'a ta Umma ta shigo da
Hussein na kuka... A hankali ta zame wayar ta
fad'i kan gado, kawai sai ta sa ma wayar kuka,
ga Kukan Hussein. Da k'allo Umma ta bita baki
sake, tasan Fure bata huce ba, ita so ma take
taji tai koh masifar irinta Maryam koh taji
sa'ida,amma ina,tun jiya take kuka da tunani.
Cikin nut'suwa Umma ta zauna a kusanta, sai ga
nan Hasna ma an kawota, tuni sai suka karade
gidan kuka, har sun ma rasa wa zasu lallasa. Sai
da tai mai isarta Umma da K'anwarta na
k'allonta kan tai shiru,sai ta hau goge ido kan ta
mika ma su Umman hannu, ba musu suka d'aura
Hussein, dan Hasna har ta gaji da kuka tasa
hannu a baki. D'uk sai suka basu tausayi. Ajiyar
zuciya tasau, tuni sai ta dan samu sa'ida ganin
yaranta yayin shayarsu, tasan koh su zasu iya
maye mata g'urbin AAA a farin ciki. Zuwa wani
lokaci har ta ware,sai d'ai d'uk ta koma marar
baki,ido kawai ne nata. Haka AAA yai ta kira ba
d'auka, gun abincintq ma suna ta neman ta, daga
karshe ta d'auka, sun hau mata lissafi kenan ta
kat'sesu da cewa su rufe "restaurant" d'in su
kaima AAA mukulli, bata jira su ba ta kashe ma
wayar d'uk tana huci. Da yamma ta fito a
wanka,d'uk kanta sai sara mata yake, har wani
jiri-jiri ta fara ji,a hankali ta nemi gefen gado ta
zauna tare da rintse ido, ji take tamkar kan zai
rabe biyu. Kukan Abulkair ne da kamshin turaren
AAA yasa ta d'an dago kai da sauri, yana t'saye
rike da Hasna duk ya marairaice fuska. Gefe tai
da kanta,sai kawai ya kut'so kai, wato tana
wanka suka shigo?amma ba mai yinkurin fitarsu
a gidan nan?... "Pretty"... A zabure ta mike ido
rufe tana tuna mishi hanyar kofa,sai d'ai ta kasa
furta komai sakamakon wani sarawa da kanta
yayi. Cikin sanyin murya tace "fita.... Da azama
ya k'wantar da Hasna ya yo gunta ganin ta fara
layi hannu rike da kai, cikin k'arfin hali da ganin
dusu-dusu tace"kar ka ra6e ni... Maganar ce ta
sarke jin K'wak'walwarta ta bar aiki,dulum take
gani ba koh dusu dusu, a chan nesa take jiyo
AAAn na kiranta yana dan girgiza kafad'arta, sai
d'ai ina,d'uk ta sake mishi jikinta tamkar wata
macacc....... By Feenat Ja'afar.
9/29/16, 3:01 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 52_Da rige rige su
Umma suka doshi d'akin jin irin kiran da AAAn ke
ma Fure, turus sukai ganin yadda AA ke jijjiga ta
amma bata koh mot'si, kawai sai Umma ta ju ya
jiki a sanyaye,ta saddakar sunyi ajalin y'arta ta,
Maryam tai saurin karasa wa tana kiranta,a
yanayinda take yasa Muh'd fita a d'akin, tuni
cikin kuka ta fara in sun kashe mata y'ar uwa
wallah su kuka da kansu... Ganin ba nasara yasa
AAA ya zame rike da Furen yana kuka tamkar
wani yaro... Ya ma manta da wani asibiti, yasan
harda sa hannunshi a mutuwar Fure.... Tamkar
had'in baki su Hasna suma suka sau kuka,
Hussein dake gado shima ya fara. Tamkar wani
zautacce haka yake surutai rike da Furen yana
kuka. Tamkar an hankad'o Ya Suleiman sai gashi
cikin d'akin, shi bai fuskanci abin da Umma ke
fad'a a waya ba,yasan d'ai tana ta ambaton Fure
cikin kuka. "Subhanallah.. Mey ya samu Furera?
Da sauri AAAn ya dago kai ido jajir, tuni Maryam
ta amshe,"yaya sun kashe mana ita ne,sun
huta... Cikin azama ya Suleiman ya kamo hannun
Furen,sai ya k'allo su, "muje asibiti, ku kamata,,
AAA ido kawai ya zira mishi,sai da ya kara fadi
kan Maryam ta d'akko ma Furen doguwar riga
suka zira mata.. Ya Suleiman zai d'auke ta AAAn
ya rigashi, kamar Yarinya ya sunkuceta sukai
waje,da ido Umma ta bisu,dan tasan sai wani
ikon Allahn Fure, ga ihun yara na yunwa. Anyi
sa'a likitoci sun k'ar6e ta taimakon gaggawa,tuni
Muh'd ya sanar ma Mama halin da ake
ciki,lallashi kawai Ya Suleiman ke mishi,dan ya
gano a halin da yake ciki, ba'a jima ba sai ga nan
Mama da Ummi. Sun samu ta farfado, sai d'ai
har yanzun ido rufe amma tana numfashi,
halamar an mata allurar bacci. A hankali ta fara
juya kanta tana mot'si da ido halamar tana son
bud'e su, cikin hankali ta bud'e idon ta sauke su
kan sling,ba abinda take ji sai karar bugun agogo
da d'an ajiyar zuciya a kusan kanta. Sai ta sauke
idonta kan waje,AAA ke rike da hannunta mai
allura ya d'aura kai a gefen gadon.. Tuni ta fara
tuno abinda da ya wakana,kawai sai ta fashe da
kuka tana ko'k'arin zame hannunta, a ka'ro na
biyu ta t'sallake rijiya da baya. Da sauri ya dago
cikin magagin bacci,ganin Furiin ta farfado yasa
yai saurin tashi. "Pretty... "Sannu..."in ke miki
ciwo?.. Ido ta rint'se tare da juyar da kanta,tuni
sai ya rikice mata, burinshi ta bar kuka koh dan
yadda Bpn ta ya hau.. "Ki yafe ni Pretty,ki
taimaken ki bar kuka ko dan lafiyar ki,dan Allah...
Shima sai ya sa mata, "kar ki maishe ni da yara
na marayu please Furii...please. Chak kukan ya
t'saya jin ya ambaci yaranta, tasan d'uk inda
suke suna chan suna neman ta ko dan abincin
su.. Tamkar an t'sikareta ta mike tare da k'allon
agogo, sha biyu na dare,sai ta cije le6e tare da
furta "Hasna... Ido ta sauke kan AAA, yadda ya
kusanto ta yana hawaye yasa d'uk sai ya kashe
mata jiki,t'sanin mace da mijinta sai Allah, tuni
sai ta ji haushin shi ya ragu ranta,hannu takai
kan kuncinshi da hawaye ke sauka tana girgiza
mishi kai itama hawayen na zuba... SO HANA
GANIN LEFI.... K'allon-k'allo kawai suke kowa na
goge ma d'an uwanshi, yasan akan Furii komai
zai indai zata d'aina fushi dashi,sai ta k'wanto
shi kafad'arta kamar yaro ta hau lallashi,tuni sai
ya kara samun k'warin g'wiwar sanarta sirrin
ranshi a kullum har sai da ya tabbatar ta saki
ajiyar zuciya ta gamsuwa da hasashen shi. Kanta
ya dago,kan ya hau sanarta kan tai hakuri bisa
fad'in da yai taje gida,yasan mey yake nufi da
hakan ba wai rashin so bane. "Pretty ina son
k'ar6a miki y'ancin ki gun su Aunty Jidda ne,su
san darajarki su martabaki, ni nasan wataran
zakiyi mamaki,dan da kansu zasu zo bikonki....
Murmushi tai tare da kara lafe mishi a jiki, tasan
fad'i yake dan ta kara sanyaya, wannan bikon sai
d'ai cikin mafarkinshi. "A jiki na ina jin su Hasna
na chan suna kuka, ni kam da an kawo min su...
Sai ta karasa da kalar tausayi,jijjiga ta ya fara
halamar rarrashi, ("I know), amma dazun kusan
takwas naje ni da Mama, an siya musu madara
da taimakon Dr,gaskiya suna da wayo,barin
Hussein, da ya ji an sa mishi (feeder) zai fara
kuka, dak'yar d'ai muka samu suka sha kad'an da
taimakon Umma da Mama sukai bacci. Ajiyar
zuciya ta sau,kan tace "Aiya,ni nafi tausayin
Hasna, mai rauni ce... Dak'yar ya lallaso ta ruwa
ya kare ya fidda Mata ruwan kan ya bata abinci
suka ci tare kan suka k'wanta. Washegari tun
asuba yaje gidan su Umma. Da Abba sukai ka'ro
ya dawo masallaci, sun gaisa yake tambayar Mai
jiki yaga sai sunke kai yake,sai Abban yai
murmushi, "Amadu shigo daga ciki, yau bamui
bacci ba sam yaran nan masu wayo.. Ai kam
suna shiga Muryar su Hussein ce ta fara amsa
musu sallamar su,Abba yace "kaji ba? Fur sunki
shan madarar sai karamar ke sha. Umma yai ma
magana suka fito parlour,ba su ko jima ba
Maryam da K'anwar Umma suka nufi gun Fure
dasu. Tana ganin yaran ta ajiye kofin shayin,
Hasna ta fara k'ar6a suna mata t'siyar tafi ji da
ita,sai d'ai ita baccinta ma take, ana bata su
Hussein tuni suka kama mikis kake jinsu ba
kuka. Sai tai murmushi tare da k'allo AAA..
Idonshi na kanta yana jijjiga Hasna a hankali
yana murmushi, sai itama tai mishi,Maryam dake
k'allonsu ta ta6e baki. By Feenat Ja'afar. 庐NWA.
Feenat.mywapblog.com
9/29/16, 3:02 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 53_D'uk da Mama ta
sanar ma su Momy Fure na asibiti ba wanda
yaje,d'uk Abba na hankalce dasu. K'wana biyu
aka sallame su da sharadin ba taron suna. Kusan
gidan Umma ya dawo wajen zaman AAA,dak'yar
yake samun lekawa Store, d'uk ragamar ya
barma su Hassan da wani dan K'anwar Mama,
d'uk sai ya same su masu amana. Sannan ya
danka ma masu kula da restuarant kan su cigaba
da gashi. "Abbansu yau na tura banki ance
account na ya d'aina aiki,sannan an sanarni da
sa hannunka, shin zan iya sanin dalili?... Abincin
shi kawai yake ci yaki tanka mata yana d'anna
waya. "Alhaji magana nake fa?... Tuni ta fara
kuluwa, dan yau k'wana biyu kenan ya d'auke
mata wuta, wanda tasan d'uk bai rasa nasaba da
kin bikon Fure da taki yi. Sannan bata tunanin yi
ko da a gaba ne. Sai da ya cinye abincin shi tass
kan ya k'allota fuska ba walwala. "Ince d'ai ni
nan na bud'e miki shi? Kai ta k'ada mishi, "toh
daga yau na rufe shi, kuma ya zama rana ta
karshe da zaki min magana akan shi.. Tashi yai
ya barta baki sake ya rufo d'akinshi, mey kenan
hakan yake nufi? Ita Alhaji zai ma wannan
wulakancin? Bayan ya hanata d'uk wasu
mukullan motar gidan sai d'ai su Huwaila su
kaisu a tasu shine ya bullo tanan? Kai ta k'ada,
"mu zuba toh. Bangarenta ta koma, sosai take da
bidar kud'i a wannan lokacin, tunaninta ina zata
samu? Dan d'ai ita kam tafi k'arfin aro... Tanan
parlour d'uk abun d'uniya ya isheta sai ga nan
Huwaila ta shigo mata da kuka. "Momy kiji Abba
ya sa an k'ulle gidan da ya ban ya kuma K'wace
mukullin motata, ina haushin wannan na wuce
cirar kud'i Momy chan ma yai blocking.. K'allonta
kawai Momyn take,mey wai hakan yake nufi?..
"Momy daga zuwa jin ba'asi ya k'ar6e min
mukulli,kuma wai wallahi kan gobe na tattare na
koma gidan mijina.... Dan Allah Momy ki taimake
ni, har mari yau nasha gun Abba... Da sauri
momyn ta k'allo ta, ta ma kasa cewa komai,
abinda Abba bai ta6a ba yau ta gani. Kan ai sati
harta Y'an aikin gidan Abba ya koresu,Momy ita
zatai girki,shara da wanke-wanke,dad'inta d'aya
wanki inji ke mata sai shanyawa, tuni Huwaila ta
koma gidan miji, nan ta tarar da wata t'siyar, dan
fir yace aure zai kara ga mai bin t'sarinshi na
rashin son yara. Ga Aunty Jidda itama ya tada
mata wuta,har gida ya bita shida mijinta, kan ta
tattara ta bashi mukullin gidanshi da mota tabi
mijinta, dan ya sanarsu tun ba yau ba shi bai
saki Jidda ba,ba kuma zai saki ba har abada...
Ranar Aunty Jidda kuka tai taima Abba kan ita
zamanta ita kad'ai yafi mata, Abba yace toh ba a
gidan shi ba. Gaba d'aya Abba ya sasu a kasa
mai wuya, an saba jin dad'i da fashaka yanzu
komai ya yanke, tun Momy na fushi dashi har ta
fara neman sulhu sai d'ai shi yace bai san
wannan ba, ta cika sharadinshi akan su kawai.
Zaune tai a kan dining tai tagumi da hannu d'aya,
sai chakala abinci take,yanzu cin abinci ya zama
sai d'ai taci dan yunwa, abinci in ba na gidan
AAA ba jinshi take salam ko da kuwa nata ne...
T'sawan sati uku kenan tai missing abincin
Fure,wanda har in taga AAA a sashenta takan
k'alli hannunshi, sai d'ai tasan Fure tai musu
nisa.... Ajiyar zuciya ta saka,kan ta ture abincin
gefe,komai ya t'saya musu chak ita da
yaranta,musamman Huwaila da Miji ke shirin aure
wannan satin, sam bai da mutunci shi,dan ko
Momyn baiya ragarma sai d'ai Abba,dan in
takamarsu kud'i shima yana dashi,amma yanzu
fur ya rufe aljihunshi gun Huwaila... Kullum cikin
yi ma Momy korafi take,gasu basu aro ko dan
ka'r ace sun gaza. Dafata akai a cinyarta, da
sauri ta k'allo gun, AAA ne d'uk ya marairaice
fuska, d'uk tausayin ta ya fara ji,dan yasan Abba
ya takureta da yawa... Kai ta k'auda, dan har yau
fushi take dasu da Mama,a ganinta d'uk su suka
ja mata Alhaji ya maisheta Talakar k'arfi da yaji..
D'uk da yasan ko ya gaidata kamar kullum ba
zata amsa ba, hannunta ya ruko yana daga
t'sugunne, "Momy nah... Cikin sanyin murya ya
kirata, bata juyo ba,amma yasan tunda bata
K'wace hannunta ba yau zata saurareshi. Cikin
nut'suwa ya fara lallashinta kan bashi da uwa
sama da ita ta yarda,yasan haifarshi ne kawai
batai ba, ta tausaya ta d'aina fushi dashi koh ya
samu komai ya tafi mishi cikin nasara... Sosai
yau ya k'wada Momy har sai da ya tabbatar ta
gamsu a gunshi baida kamarta ko da kuwa Mama
ce... Kai ya d'aura cinyarta har da hawayenshi,
"Sam bani kaunar ganin ki cikin wannan yanayin
Momy na,nakan shiga wani hali in na ganki ba
k'ya walwala.. Cikin siyasa yai ta nuna mata kan
damuwarta tashi ce har kullum. "Momy ki ce
komai kin isa,amma dan Allah ka'r ki rabani da
yarana da Mamansu, ina neman ki yafe musu in
sun sa6a miki,ki musu afuwa ki ce su
dawo,nasan ke mai son farin ciki na ne a kullum
Momy, amma in kinga basu dace dani ba Momy
zan bi d'uk yadda kika ce,zanyi... Ya karasa yana
saukar mata da hawayenshi bisa kafarta...
Sassanya ne Ahmad, ko a yaranta batajin dan
wanda bai kaunar ganin damuwarta sama da
AAA, tasan ba wanda yake jin maganarta sama
da AAA, sannan bazata ce ga abin da Fure tai
mata ba har ta ji bata kaunarta,gashi tana mata
ladabi iyakar iyawarta, koh dan duba ga yadda
sirikarta kishiyar Rukayya ke yi a gidan, gata d'ai
y'ar masu kud'in ce,kuma jinin sarauta,amma
sam bata ganinsu da daraja bare mutunci,
asalima ba gidan su take zuwa ba ko da abu ne
kuwa ya faru, ga nan mijin Huwaila, arziki kamar
suyi ihu amma ba k'wanciyar hankali, baya
darajasu su iyayen Matarshi. In d'ai haka auren
mai arziki yake toh tabbas tasan g'wara su
Fure,masu karamin k'arfi amma suna k'yautata
musu iyakar iyawarsu, sun san darajarsu, sannan
bassu girman kai.. Sai yanzu ta banbance dabi'ar
talaka da mai kud'i... A dalilin su Fure ta
banbance t'sakanin t'saki da t'sakuwa... Ajiyar
zuciya ta sau, kan ta kai dubanta kan AAA da har
yanzun yake hawaye yana kuma nema musu
gafara shi da Furiin shi, a hannu takai kan sumar
kanshi tana shafawa halamar yai shiru,sai ya
k'allota, murmushi tai mishi tana girgiza mishi kai
tare da goge mishi hawaye.. "Momyn ka na
kaunar ka da iyalanka Ahmad, tabbas nasan kai
D'a ne,har da kari, na gode sosai sannan zaka
sha mamaki. Murmushi yai wanda har
hak'waranshi suka baiyana,sai ya kara k'wantar
da kanshi yana k'wararo mata godiya tana
murmushi. Bai tunanin zai samo Momy da y'ar
guntuwar ban hakurin nan ba... Mama da tazo
ban hakuri itama yau dan ta gaji da wannan
gabar sai ta goge idonta, fatan ta Allah yasa
Momy ta gane kuranta game da Fure. By Feenat
Ja'afar. 庐NWA. Feenat.mywapblog.com
9/29/16, 3:04 AM - Queen Safiyyert馃憫: [5/17, 10:20 PM] Feenat Ja'afar: "JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
54_"Ya zanyi Sis Fatee? Abinda hakuri bai baka
ba,nasan rashin shi ma bazai baka shi ba, adu'a
ta a kullum Allah ya shirye su su gane...
Dan t'saki Fateen tai, "Ba komai kake ma hakuri
ba Furii,mutum shi kad'ai ke nemawa kanshi
y'anci, ace yau har sati uku ba ko kayan suna,
toh mey suke nufi? Murmushi Furen tai, dan bata
sa a ka ba,wai an T'sikari ka'rkausa.. Maryam
dake gefe da sai hararar Fure take tace "ki barta
Aunty Fatee,ki ma d'aina bata yawun bak'in ki,
dan ni tun daga yadda ta sau jiki da mijinta
nasan tabbas Ya Fure batta zuciya, tunda nan ya
korota gidansu cikin bainar jama'a.
K'allon Maryam d'in kawai take,yadda take ta
kumfar baki, sai ta k'ada kai, "ba zaku gane inda
na dosa bane Maryam.. Rayuwa y'ar hakuri ce,
AAA na da dalilinshi na yin hakan, believe me...
Har kusan magriba suna zaune tattauna
mat'salar gidan su Momy, kukan su Hasna ne ya
kat'se su suka fara aikin lallashi.
K'allon yaran take,yadda sukai bul bul dasu,barin
acici su Hussein.
"K'allon yaran nan kad'ai ya isa mantarni d'uk
wani bak'in cikin rayuwa Allah... Ku manta da
zancen su Huwaila, kema Maryam ki kula mijinki
fa yaron ki,sosai na kula har yau baki sakar ma
Abulkair, ki sani basu laifi, haka Muh'd bai da
laifi,ki fuskanci zahiri,mijinki na son ki, kar ki fara
huce haushinki kansu..
Karan nan da halamar ta d'au zancen Furen,
suna cikin haka suka ji a chan t'sakar gida
Umma na fad'in Sannun ku da zuwa Hajiya
Maryam... Da sauri Fure ta k'alli Maryam, tabbas
muryar su Momy take ji, da sauri suka tashi
kowa rike da d'aya suka leka waje, su d'in ne
kuwa.
Tuni Maryam ta had'a girar sama da ta kasa ta
kama k'ugu da hannu d'aya tana girgiza ganin irin
k'allon da su Huwaila ke ma gidan tasan ba
zuwan mutunci sukai ba, "mey kuma aka biyo a
ma ya'yan masu t'siya har gida?... Da sauri
Momy da Umma suka k'allo Maryam.
"Umma ki sanarsu su bar mana gida kan muyi
ta'asa dasu wallahi... Da sauri Umma ta kat'seta
"Maryam... Ban son shashancin banza...
T'saki Huwaila tai,kan ta harari gun su Furen, "ba
dan Momy ba wallahi da ba abinda zai kawo ni
gidan nan... Har meye abin tinkaho a wannan
akurkin? Cikin tunzara Maryam zatai kanta Fure
ta rike ta,, Momy kai kasa bata hana ba, Umma
ta sau baki, sam batasan yaran bassu tarbiya ba
sai yau...
Gaban Momy Fure tazo, har kasa ta tsuguna ta
d'aura mata Hussein a cinya, ta juya ta k'ar6o
Hasna da Hassain ta jere su kasan dardumar a
gaban Momyn.
Kowa k'allonta kawai yake, cikin nut'suwa ta
fara fad'in "Momy, dan Allah yau ka'r ki
kat'seni,ki barni at least na fad'i son raina, ki
bari yau d'aya nai magana in yaso in na gama ki
min hukunci koh da na marin ne, wallahi zan
d'auka...
Ta karasa kamar mai shirin kuka.
"Huwaila.. A wulakance ta k'allota tana
y'atsina,kai in ka ganta d'uk ta fita hankalinta ta
fige, d'uk dan tashin hankalin gidanta. Murmushi
Furen tai tare da girgiza kai, "kin san Allah
d'aya? Toh wallahi mun fiki k'wanciyar hankali..
Baki ta Huwailan ta ta6e, "ina wata k'wanciyar
hankali a talauci?..
Murmushi Furen ta sake, "haka ne, amma zai fi
k'yau ki t'saya a talaka a yanzun da wannan halin
da kike ciki.. Zai fi miki k'wanciyar hankali
zaman ki a JUYA,sama da zama mai haihuwa
gun miji... Kowa ya kalle ki yaga marar
k'wanciyar hankali, ga dai daular, amma kin gamu
da gamanki, kin gamu da wani irin Miji, wanda da
ke mai hankali ce da kin gane Ayar da Allah ya
saukar kanki... A tunzure ta k'allota,sannan ta
k'alli Momy, kanta na kan su Hasna.
Sai ta samu kanta da kasa fad'in kalma ko d'aya
ga Furen.. Hakan ya bata damar cigaba da
bayaninta.
"Kasantuwa ta a JUYA a da a gunku,hakan bai
hanani samun soyayyar Miji ba,naci takaicin
ku,d'uk a ban haihu ba,na zata in na haihu gori
zai kare ma d'an kada.. Ban san aibu na gare ku
ba, ban san da mey na rage ku ba?..ban sani ba
Momy.
"Momy in har na ta6a sa6a miki dan Allah kimin
afuwa... Bazan iya kankare asalina ba, bamu
zama d'aya ba, ba kuma zamu zama ba.. T'sit
kake jin su, tamkar wasu mummunai sun kafeta
da ido,mamaki ne koh meye oho.
By
Feenat Ja'afar.
[5/17, 11:31 PM] Feenat Ja'afar: "JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
55_Kan Aunty Jidda ta dawo,cikin aminci ta fara
mata magana.
"Aunty Jidda.. A gani na ke ce mutum ta farko
da ya kamata ace kin min uziri yayin da ban
samu haihuwa ba.. A gani na kalmar nan ta
JUYA bai kamaci fita a bak'in ki ba ma.
"Na sani da kila ke baki gano matsayi d'aya Allah
ya bamu ba a da, wallahi sai nake ga kamar abin
kunya ne kai ma mutum gorin abinda kaima baka
samu ba, ko dan ance g'wanau bai jin warin
jikinshi sai na wani... Kiyi hakuri Aunty Jidda, ba
fitsara nai miki ba.. Amma kinfi chanchata a
kiraki da JUYA sama dani, ban fa ja da ikon Allah
ba.. Na fad'i raina ne kawai,kiyi hakuri in na 6ata
ranki.. Ta karasa tana mata murmushi.
Kan su Huwaila ta dawo,
"Bari kuji,ba wai dan ina da lokacin ku bane zan
tanka muku,kai ta girgiza,"nasiha ce,Kila tai
muku amfani,,
D'uk k'yaun ka,d'uk dukiyar ka,da d'uk wata
K'awa ta duniya, mud'in kika rasa halin k'warai,
wallahi, "u r nothing, don babu ma ta fiki mat'sayi
gun Allah,
"Ku kuna kawai hoping 4 dis Duniya, wacce ba
komai acikinta face t'sant'sar nadama,da da na
sani.
Ku sani...
"Wani yana chan a k'wance a asibiti ba lafiya,kila
ma ko kudin sayan magani bai da shi, wani gidan
sa yau ko na safe basu samu abinci sun sa a
bak'in sallati ba,wani ko kud'in gidan haya bai
dashi, amma ku Allah d'uk ya baku wannan.
"Sosai k'yawawa ne Ku,farare" hurul ein" koh? Da
ido ta kafe su, jin basu tanka ba yasa ta k'ada
kai.
Tabbas banni k'yau,
sai d'ai ku sa ni, ban ta6a dana sanin hakan
ba,cos ina duban na kasa dani sannan na gode
Allah,saboda yayi min Ni'imar da bai ma wasu ba,
yai muku k'yaun da bai ba wasu ba,ya baku lafiya
da bai bawa wasu ba,ya baku d'uk wani farin ciki
na duniyar nan, "mind you, ba fa wai dan yafi son
ku bane ya muku hakan? Kai ta girgiza,"no,wal
lahi talaka,daya riki Allah da manzon sa,sai ya
sami mukami babba a gun Allah wanda ku ba
d'ayan ku ba zai samu ba.
"Domin da kanshi yace wanda yafi wani a guna
shine wanda yafi tsoro na,ba wai wanda yafi
dukiya da k'yau ba, amma "instead of you to
thank Him,,umm..um u r ungrateful... Kun gode
mishi ne ta hanyar gorantawa wanda ya tauye.
Ku sani,ak'wai mutuwa,
"and wallahi,you will leave all these behind.
" In kin ta6a jin "k'aruna" wanda a tarihin duniya
ba ai mai kud'in shi ba, ba kuma za ai ba,
amma da ya mutu sile biyar bai tafi da ita
ba,daga shi sai halinshi, yanzu kam arzikin da
komai babu, da an turmusa ki kabarin ki k'yaun
shi zai fara zag'wanye wa,karshe ki zama kasa
abar takawa.
"Kinga ba bu Alfari,babu Dukiya,babu
k'yaun,yanzu kam sun zama kasa.
"Toh ku fad'an, wanda zai zamu haka a
gaba,meye nashi na tunkaho da wannan
duniyar?? Kai ta girgiza..
"Malamai,wallahi you better seek ur "Jannah"
sannan ku gode Allah da baiwar da ya muku, ta
hanyar fad'in Alhamdulillah, ba wai ta gorantawa
wanin shi ba,da nuna isa da fariya..
Shiru tai, jin sallamar Abba cikin gidan, tunda
yaci ka'ro da motar AAA ya sanar shi su Momy
ne jikin shi yai sanyi, sai d'ai daga shi har AAAn
sun sha mamakin jin gidan t'sit sai tashin nasihar
Fure cikin nut'suwa.
A hankali ta tashi tai gun Abban d'uk suka bita
da ido.
Kayan hannunshi ta k'ar6a cikin girmamawa tana
leka wa, sai ta dago da murmushi, "har kullum
ina alfari da kasancewar Abban mu makanike
mey ci da gumin shi, kun ganshi nan, a kullum
cimarmu mai dad'i ce, dan ta Abba ba mai cin
k'wananen abinci, burinshi ya samu ya kashe su
kanmu, dan haka a kullum ya zama abin alfaharin
mu,dan haka ne nake yaki da d'uk mai neman
taka min shi...
Jin kuka zai K'wace mata yasa da sauri ta lafe a
gefen kafad'ar Abban,d'uk sai ya kara kaunar
Furenshi, tabbas sun cika yara na halali,masu
takama dashi a d'uk yadda yake..
Tashi Maryam tai tana goge hawaye tai gun su
Abban,d'uk sai ya hau lallashin su.. Ba zata suka
t'sinkayi muryar Ya Suleiman.
By
Feenat Ja'afar.
[5/18, 12:31 AM] Feenat Ja'afar: "JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
56_"Yanzu kam komai ya kare ai.. Dan haka ku
tashi tun da guntun mutuncinku Hajiya ku
tafi,d'uk din su ba wacce akai ma auren sadaqa..
Rayuwar y'anci muke yanzun, haka nake bid'ar
ganin k'anne na ciki.. T'sit sukai ba mai mot'si
cikin su, ciki ya karaso cikin bacin rai, da dan
k'arfi yace "ku tashi nace koh?.. T'saki Rukayya
tai, kan ta hau neman tashi, "Ga'iyar... Saukar
mari taji yasa da sauri tai shiru ta zauna d'ai d'ai
rike da gun,Momy ce.
Hannu ta nuna ta dashi, "ka'r na kara jin bak'in
cikin zancen wani anan... D'uk k'allonta suke
cikin mamaki musamman Huwaila da Rukayya da
Fure.
"yanzu Momy akan wa'enan Mat's... Wani marin
ta kara sakar mata,wanda ba shiri ta g'imtse baki
tana shafa gun.. "Ki kiyaye ni,in ba zaku iya shiru
ba ku tashi ku ban gu.
Kamar masu jira da suka d'au jakukkuna sukai
waje suna kunkuni. Ita d'ai Aunty Maryam ido ne
nata, yayinda Aunty Jidda takaicin duniya ya
isheta ganin abinda Momy tai,gashi tace bata
yafe ba in ta tofa tun suna gida.
Hawaye Abban ya goge ma su Fure kan ya juya
ya koma yana mai kiran Ya Suleiman, fatan shi a
wanye lafiya.
Tashi Momyn tai tazo inda su Fure suke, ido
kawai Fure ta zuba mata, Maryam kam kai ta
k'auda, dan Allah yaga taki jinin Momy.
Hannu ta daga zuwa fuskar Fure dake hawaye,
da sauri ta rint'se ido tana mai jiran saukar mari
a kuncinta,yayinda da sauri AAA ya ju ya baya
shima ya rufe ido.. Sai d'ai har wani lokaci bai ji
saukar mari ba,hakan yasa ya d'an ju ya.
Abinda ya gani ne ya sashi juyowa gaba d'aya,
Momy ke sa hannu tana goge ma Fure hawayen
fuskarta tare da girgiza mata kai halamar ta
d'aina kuka, da sauri ya sau ajiyar zuciya tare da
washe baki yana murmushi.
Kan Maryam ta koma wacce ta zumburo baki tai
gefe da kai...
"Kuyi hakuri kunji ya'yan nan.. Takanas nazo
bikonku ku koma... Nasan ba ku samu yadda ya
dace ba a zamanku na baya ba gun mu.. Ban rike
ku sirikai ba sam, amma ku kun rike ni uwa...
Shiru tai tana k'allon su,wanda su ma k'allonta
suke baki sake, wai Momy ke basu hakuri? Kuma
cikin sanyin murya? Ido Fure ta ka'rkad'a, tana
fatan in mafarki ne ma lalle ta wat'sake...
Tamkar Momy tasan tunaninta ta ruko hannunsu
tana murmushi suka zauna.
Chan ta nisa ta fara magana,"Furera... Ido Fure
ta rint'se, a ka'ron farko da Momy ta ta6a kiran
sunanta.. Hakuri ta fara basu dasu Umma cikin
nuna nadamar abinda tai musu,da alkawarin ba
maimaici InshaAllah.
Tun suna ganin abin kamar da wasa har suka
ware da yardar lalle Momy tai nadama,sai
rarrashin Hussein take dake kuka tana fad'in
"wannan na Umman ku ne, nawa mai gidan gashi
nan.. Tana nuna Hassain, kamar mai jira shima
ya kama kuka,baki sake tace "au,au,kaima hakan
take?
Banda murmushin jin dad'i ba abinda Fure ke yi,
a hankali ta daga kai ta k'alli gun da AAA
yake,shima idonshi akanta yake,tuni ta hau mishi
godiya cikin yaran su nasu kadai da kurmanci, ido
ya lumshe mata halamun ya ji dad'i.. Sai ta
kawar da fuska tana murmushi. Tasan wannan
aikin na AAAn tane, a karshe yai nasarar gashi
har gidan Momy tazo wai bikon sun a zahiri ba
mafarki ba,tuni ta kara jinjina wa hakuri.
Ai Aunty Jidda tuni ta bi bayan su Huwaila, dan a
ganinta Momy ta ma gama badasu gun su Fure,
gashi Fure ta sha da ita ba damar magana,sai
Taxi suka hau dan da motar AAA kad'ai da Aunty
Maryam suka zo, ita kam Rukayya gida ta wuce
tana tunanin yadda yau Momy ta mata,kai ta
girgiza.. Su zuba toh.
Har dare Momy tana gidan ita da AAA, Aunty
Maryam ta tafi, sai ga nan Momy tana zukulkular
tuwan hatsi miyar d'any'ar ku6ewa tana santi..
Har ta kasa shiru sai da ta tofa. Shi dai AAA
bak'in nan kamar gonar audiga dan murna, yasha
mafarkin ranar nan sai yau tazo da ikon Allah,
fatan shi Allah sa su Aunty Jidda ma su gane.
Ba karamin farin ciki Abba yai ba da jin zuwan
Momyn,ganin yadda AAAn shi ke farin ciki yasan
yau Maryam ta wanke laifinta, hakan yasa
Washegari da kanshi ya shirya dan zuwa har gida
kara bada hakuri, abinda bai ta6a ba sai kansu
Fure.
Lokacin Abba ya dawo suna a t'sakar gida kamar
kullum Familyn g'wanin ban sha'awa AAA yai
sallama.
Jin da wa yake tafe yasa su tashi zuwa neman
mayafi, da t'sabar kunya shima Abba suka
gaisa,dan bai ta6a tunanin zuwa domin gaisuwa
ma sirikin nashi ba koh a hanya, asalima shi bai
san waye Abban su Fure ba koh a hanya, sai d'ai
da mamakin shi yaga Muhammad ne ma, cikin
mamaki yake k'allon Abban,shikam murmushi
kawai yake.
"Wai da gaske ne koh ido na ne Muhammad?
Murmushi Abban yai mishi, sai Abban su AAA
yace ma Ahmad d'in "lalle ka lalubo zumuncin da
Baba na, dama su Furera yaran ka ne? Ikon
Allah, gaskiya har naji kunya, nasan da Nasir na
raye da yau zan d'au query, shi d'ai Abba
murmushi kawai yake.
"Ke nan kai ka gane ni Muhammad, kai ya k'ada
yace "sosai ma Yaya,tun a auran Furera na gano
dangin Nasir ne ke nema, toh a gun d'aurin aure
na gano ashe ma kaine Abban Ahmad.
Abba yace "ikon Allah, amma baka k'yauta ba
Muhammad, sosai Hajiya tai k'ewar ka har ta bar
duniya....
Shi d'ai AAA an sashi t'sakiya, ya k'alli Abban su
ya k'alli Abban su Fure, da halama yana neman
karin bayanin a fiddashi duhu.
By
Feenat Ja'afar.
庐NWA.
9/29/16, 3:05 AM - Queen Safiyyert馃憫: [5/18, 11:45 PM] Feenat Ja'afar: "JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
57_Irin firar da sukai ne ya gane sun jima da
sanin juna,koh dan yanayin yadda kowa ke
tambayar bayan rabuwa.
A mota d'ai AAA ya kasa hakuru yai tambaya,
cikin murmushi Abba ya sanarshi ai sun san juna
da Abban su Fure da jumawa tun zamanin jami'a,
a dalilin k'aninshi Nasir sukai sabo sosai,d'uk da
ba t'saran shi bane.
"Sosai sunyi abota da kawunka,wanda har ya
zamana Hajiya ta d'aukaki Muh'd d'in, dake shi
Nasir ba mai nisan k'wana bane tun bayanan ban
kara ganinshi ba...
Kai ya jinjina, yana mai farin cikin wannan rana
da jiya,burinshi Furii ta dawo mishi dan zaryar
nan d'aurewa kawai yake, amma da kunya.
Tuni Abba ya dawo ma su Momy komansu harda
karin kud'i a (account), har sashen Mama Momy
taje dan jin shawarar irin kayan da za ai ma Fure
na suna, dan fa fur tace sai ansha shagali kamar
na kowa, sosai Maman tai murna,har ta kasa
6oye wa.
Aunty A'i Momy ta bama k'wanigilar had'a kayan
goyon Furen, tuni kuwa ta hau 6adda kud'i tana
narko ma (Babies) da Furen kaya na azo a ga.
Sosai sunyi rawar gani,dan naira ta ci kasa.
Baki kawai su Umma suka zira lokacin da kaya
ya iso musu, tabbas gidan su AAA sunyi wuta.
Haddadiyar walima suka had'a a harabar gidan
su AAA, su Fatee kan gaba Wai dan ma ciki yai
yawa.
Lalle ne bayan wuya sai dad'i, ga nan Fure sai ji
da ita da yaranta suke,ita kam bata cewa komai
sai godiya ga Allah.
D'uk da su Aunty Jidda su basu yadda makaman
yakin nasu ba a kanta,amma sosai ta sarara,dan
fur Momy ta toshe d'uk wata kofar da zasu
muzgunawa Fure, ga kuma tsoron ka'r Abba ya
kara k'wata musu ta da.
Tuni Maryam ta koma, amma gida daban Muh'd
ya sa ta,yanzu kan ita da Hassana sai gani daga
nesa.
Lokacin arba'in d'in su Fatee ta juye nata, sai
abin ya zama biyu,ga shirin komawa gidan
AAA,ga jelar gidan Fatee.
Tuni likafa ta hau,yanzun kam kowa a dangin
Salman nanike mata yake son yi, sai d'ai ita tace
ina, wai takai-takai.
Huwaila d'ai aure yaki dad'i, dan fur Miji ya juya
baya shi sai amarya, wai ta zama chus,ga gida
d'aya ya gamasu da kishiyar, da ta hau mata
fallin amarci take tada hauka, a haka har ta
k'wata ya jibgeta had'i da saki ya kuma bar
kasar.
Da wannan Momy ta kara tir da wani auren mai
kud'in.
Yanzu kam Rukayya ita aka sa gaba, dan tuni
lakabinta gun su Aunty Jidda ta fara amsa sunan
JUYA... Ga kishiya mai dan uban isa da gadara,
ita a dole jinin sarauta, ita ke da (remote) a
hannu sai yadda tace ai ake yi, da ta nemi yi
mata rashin kunya zai taka mata burki,dan fa wai
yana ji da Matarshi tamkar t'soka d'aya cikin
miya...
Ga sharadin Babanta na in ta kaso aurenta toh
kar ta tunkari gidanshi, ga Momy tun daga abin
Fure da tai mata zuciya itama Momy ta nuna
kamar ba ai ruwanta ba.. Tun Rukayya ta shiga
t'saka mai wuya, ko ina ba dad'i, ga yaran gidan
kadai sun isheta hawan jini, rayuwar dai sai a
slow gun Rukayya.
Ita kam Aunty Jidda tuni karan nan Abba ya
bud'e mata wuta kan sai ta koma gidan
mijinta,tunda yace shi bai Saki ba.
Karshe tana ji tana gani ta koma gidan da tai
rantsuwar ba komai cikin shi.. Wanda a zahiri
jarabar uwar mijin su yasa taki auren fur,dan
sosai take wanke ta ciki da bai d'uk wai ta cika
musu gida ga ba wani fus,.. Amma dake Dan
Adam ce ita wai har take huce takaicinta kan
wata.
**********************
K'wance take cikin d'aki gaba d'aya yau jinta
take wani iri, dak'yar ta samu ta lalla6a su
Hussein ta basu ball kan su fita sui wasa zata
huta.
Tana t'saka da bacci ta zabura har tana shirin
fad'o wa a gadon, jiri take ji,ganan kuma karar
zubar abu,wanda tasan babu tantama daga
kitchen ne aka zubo mata (plates) suka fashe.
Kawai sai tasa kuka tana mai dan buga gado ba
koh hawaye, kai da gani kasan kukan 6aci ne,
yara tamkar beraye kullum cikin 6arna suke
mata...
By
Feenat Ja'afar.
[5/19, 12:50 AM] Feenat Ja'afar: "JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
58_Parlourn tai dank'wali a hannu tana sakar ma
su Hassain harara,tuni suka fara raba ido ya 6era
a buta..
Hussein da ke a bak'in kitchen rike da ball yace
"momma hakuli...
Harara ta kara mishi rike da k'ugu, kan tace "mey
ya kai ku kitchen? K'allo Hassan yai sai ya k'allo
Furen..
Cikin maganar yara suka ce ai ita tace su je sui
ball,shine suna ball ta fad'a kitchen ta bigi
farantin kofuna..
Kai ta dafe tare da fad'in "oh Allah,, wato g'wari-
g'wari kullum zan ta muku kan ku gane ummm?
Parlour ne waje? Kai suka k'ada mata.
Sai ta fara dube tana "yau zan zane ku son rai ba
mai k'watar ku... tuni suka fara t'sula mata ihu
ganin ta zari tsinken k'wak'wa suna kiran
Daddy...
Zagaye suka fara ta ma kasa kama su, bak'in
nan kuwa yaki mutuwa da ihu tamkar ma d'ukan
nasu take.
Shigowarshi kenan ya fara jiyo ihun yaran, ko
karasa cire mukullin mota bai ba yai cikin
gidan... Ina,ai tuni sun galabaitar da ita dan
shegen ziliyarsu, kasa tai tana haki tana nuna su
bulalar hannunta..
Da d'an gudugudun shi ya shigo, ai suna ganinshi
suka runtuma gunshi suna nuna mishi Furen,
ganin bulalar hannunta yasa ya fara daga
rigunansu ya ga koh ta dake sun.
Shiru kakeji sun bar ihun,tuni ya hau fad'a yana
ta kiyaye shi kan dukan yaranshi, dan takaici
kawai sai ta sa mishi kukan shag'wa6a, harda
buga hannu kan (carpet), tamkar yarinya ta koma
mishi, sai ya sau baki yana k'allon borin
nata,suma su Hussein k'allonta suke d'uk sunyi
narai narai da ido.
Bai nufa ba ya ji sun sa mishi suma kukan, sai
sukai gun Momman d'aya na girgiza mata kai
halamar tai shiru sun d'aina, d'aya na goge mata
idon da ba koh hawaye.
Kawai sai ya harde hannu yana k'allon su.
Shiru tai tai tana k'allon su,jin yadda suke ta
fadin sun d'aina, cikin shag'wa6a tace "promise?
Da sauri suka k'ada kai, sai tai murmushi tare da
janyo su.. Tuni kuma aka hau dariya jin
chakulkulin da take musu.
Kai AAAn ya k'ada yana musu murmushi ya juya
kashe mota.
Yasan 6arna kenan sukai mata.
A kitchen ya t'saya jin hayaniyar su,k'washe
fasassun kufunan take tana su mat'sa kar su
taka. Kiran su yai suka fita,tuni ya had'a kowa
da t'sarabar shi suna t'sallen murna yace su je
gun Baba mai gadi kan ya fito suje gun Hasna,da
murna suka fita shi kuma yai d'aki.
Jin an bud'e d'akin yasa ya k'alli kofar,rufe wa
tai kan ta jingina kanta a jiki tana K'allonshi, d'uk
ta marairaice mishi fuska halamar ya agaza
mata.
Rigar da ya cire ya ajiye kan ya tako gunta cikin
lallashi, a gefen gado ya zaunar su tai lamo
jikinshi.
("My Furii what's wrong?) Uhnmm?.. Cikin
marairaita ta hau ta6e baki kamar zatai kuka,tuni
ya hau lallashi tamkar Hasna ke gabanshi, rad'a
ya fara mata yana ka'r ta sare man tun a su
Hussein... Kai ta k'ada, tasan bazai gane ba ne,
amma tun yanzun har ta fara galabaita da cikin
tun kan yai k'wari.
Lallashi yai ta yi kan ta gode Allah da k'yautar
da ya kara mata, ka'r ta sare tun yanzun..
Kai ta k'ada, "hutu nake so fa Daddyn su, yaran
nan sunki su barni, ni kam a kaisu Allo private ta
tun safe sai yamma koh na huta da kiriniyar su
Hussein... Dariya yai, kan a hankali ya k'wantarta
ya g'yara mata pillow, har da ja mata bargo.
Kanta ya shafo yana mai bata (favorite)nata
cikin nut'suwa.. Tuni har ta fara lumshe ido da
jin dad'in sautin abin.
Jin tai shiru yasa yai tunanin tai bacci ne, cikin
nut'suwa ya duk'o ya dan bata (peck) tare da
g'yara mata bargo.
Kayanshi ya d'auka cikin sanda ya bud'e kofar
dan gudun kar ya tada ta yai dakinta dan wanka.
Da k'allo ta bi bayanshi ganin yadda yake jan
kofar a hankali, sai tai murmushi.
By
Feenat Ja'afar.
[5/19, 7:09 AM] Feenat Ja'afar: "JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
59_Hannu takai kan cikinta tana mai shafawa,
tabbas bazatai butulci da Allah ba dan ya bata
ciki a kusa,ai ma ta raka, tunda su Hasna sun
kusa shekara uku,tasan yasan zata iya ne ya
bata, fatan ta su rabu lafiya.. A hankali tai bacci
cike da kaunar gidan ta da mai gidan.
Basu suka dawo ba sai kusan taran dare,da kaya
niki-niki.
Tana zaune kuma d'uk sai kewarsu ta dameta,
sai maka mishi kira take kan su dawo ta
huta,murmushi yai,dan suma Hasna ta mat'sa
mishi da fad'in Momman ta.
Da sauri ta tafi gunta kuwa tana mata oyoyo,
kanta ta shafa da yasha (twists-stick) tana mata
sannu da zuwa.. Ita kam batta da k'warafniyar su
Hussein.
***********************
Rayuwar na ta kaima Fure,ta haihu lafiya su
Hussein sunyi k'ani, zo kaga k'walo kusa da
baby,wai nan d'uk murna suke.. Kawai sai ta
tasasu gaba tana k'allo cikin murmushi, AAA na
d'aura ma Hasna babyn suna dariya.. Wai yau ita
ke da yara hudu a rayuwa??.. Tuni ta fad'a
duniyar tunanin da,har AAAn ya kula da ita.
K'allonta shima ya hau yi,bai san karan nan da
mey zai sakama Furiin shi ba? Ya d'ai san a chan
kasan ranshi kaunarta kad'ai ke kara nunkuwa da
k'yawawan yaranshi da take sum6ulo mishi, abin
sai d'ai godiya ga Allah kawai.
K'wanan su d'aya aka sallame su,tuni gida ya
debi su Fatee da nata bataliyar uku,yanzu kam
zumunci ya kara yawa har sun zama y'an uwan
juna.
Ita kam Fure bata cewa komai ga Allanta sai
godiya a kullum, ga bud'I da take samu gun
abincinta, har yau tana nan da bama su (special
dishes) d'inta.
Yanzu kowa mutuntata koh dan tsoron Momy da
Abba dake bala'in ji da ita da iyalanta, ga kuma
yadda ita kanta ta bunkasa ta zama hajiyar
kanta.
Sai gani sai kuma harara daga nesa, dan yanzu
bata ragarma uban kowa t'sakanin su Huwaila,
take suna fad'a mata d'aci zata basu mad'aci.
Sai ya zamo suna shakkar fad'a a gabanta.
Sunzo barka har gida suna d'an y'atsinar nan da
ta zame musu tamkar dole, aciki suke mata
barkar, ita kam Rukayya ji take kamar ta d'auke
babyn, d'uk tai laushi.
Tashi tai tana sanarsu zata shiga wanka dan tun
dazun aka kai mata ruwa. Kai kawai suka daga
mata.
Ta gama cire kaya zatai wanka ta jiyo maganar
su kasa-kasa.
"Wa ya ga kaza uwar ya'ya.. Ina ga kan a
shekara goma sai ta had'a ma AAA garke..
Cewar Huwaila.
Tana jiyo Aunty Jidda na fad'in "su d'ai suka
sani, ke meye naki?
Dariya Furen tai, tare da fad'in.
"Toh fa! "From fan to fire" daga ''JUYA'' na zama
"K'aza" uwar ya'ya? Murmushi tai tare da k'ada
kai, D'an Adam sai ka barshi, amma sam baya
godiyar Allah sai kalilan daga cikin su, w'ankanta
ta fara tana jinjina halin Mutum,lalle ne in ta biye
ta mutum toh itama sai an kaita an baro. Bata
haihu ba an kirata da JUYA.. Ka haihu ance maka
Kaza uwar ya'ya.
Mutum! Mutum!!, ba mai iya mishi sai Allahn shi
kad'ai....
ALHAMDULILLAH.
Na gode Allah da yasa naga karshen wannan
littafi (JUYA),Ubangi ya sa mu amfana da
darrusan da ya koyar mana ciki.
Never loss hope,and trust in the power of du'as,
InshaAllah Allah will grant you everything you
wants as long as it is good for you...
In har kaga baka samu ba,toh ka d'auka babu
alkairi acikin rayuwar ka kai da abin...
Dan With God,everything is possible...
MashaAllah...
Nafisa Bashir Tanko (Feenat Ja'afar) ke muku
fatan alkairi... Muyi Ramadan lafiya, tare da
muku albishir na barka da sallah Novel d'in
gaba,mai suna....
"A BAK'IN AUREN KI"...
Love you all....
By
Feenat Ja'afar.
庐NAGARTA WRITER'S ASSOCIATION.. (NWA).
Feenat.mywapblog.com

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *