Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Sunday, July 8, 2018

RAMLAT Yar Tsintuwa Complete Hausa Novel (Hausa Novels World)

adsense here
RAMLAT Yar Tsintuwa Complete Hausa Novel (Hausa Novels World)
      Copied By
HAYATU BABA ZUBAIRU
        (admin
       Novels villa
     Duniyan novels
   Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
          And
Cool novel, makeup and cooking)

      WHATSAPP NO:
       07039625239

🍀🍒🍀
              *RAMLAT"*
           _Yar Tsintuwa_
                          🍀🍒🍀

*_Written BY raheem jEgs📚_*

*Da sunan Allah mai rahama mai jink'ai tsira da Amincin Allah su tabbata ga Khairul Anbiya wato Annabi muhd (S A W) ya Allah ka k'ara d'aukaka darajar masoyan mu bayayyananni da boyayye*

_NAYI WANNAN LITTAFIN NE DOMIN SANYA NISHAD'I DA FAD'AKARWA GA AL'UMMA ZARGI MUGUN K'ULLI "BANAYI BANE DANCIN ZARAFIN WANI/WATA BA IDAN KUMA KUSKURE YA BIYO BAYA ALLAHU GAFURRUN RAHEEM._

              🍒 _RaMlaT_ 🍒
                        *1_5*

 *_( YOBE STATE )...._*_misalin Karfe 8:15am nasafe zaune yake acikin babbar Office d'insa ga wata shahararriyar Lapton agaban sa ba abinda yakeyi face dube2 akan wani DOCUMENT wanda dukkan wani sirri na tattalin arzikinsa da filayen sa campanoninsa da tsaresarensa duk yana cikin wannan document da yake bincike aciki,_

Amma abin mamaki duk wannan abin bashine gaban sa ba sai tunani da kuma tsintsar tausayin karamar 'yarsa da yabaro a gida wadda bazata wuce shekaru 5 zuwa 6 ba, "Alhj *Hisham A. Ahmad* kenan wanda yayi k'aurin suna Acikin jahar Yobe state.

Mutum nea mai kyakkyawar zuciya son jama'a kyautatawa da kuma kawar da azzaluman mutane bai d'auki duniya komaiba hakan yasa yakeda tarin mak'iya masu bibiyarsa akan su kawarda shi wannan shine dalilin da yasa akoda yaushe yake tausayawa 'yarsa domin yasan za'a wayi gari wata rana mak'iyinsa sun kawarda shi
Wannan shine.

_K'wankwasa kofar akayi a hankali yad'ago kai yace "YES wani Alhj nea yashigo cikin manyan kaya babu alamar fara'a a fuskar kallo daya zakai mada kagane mutum nea mai babbsn matsayi a gaunati a fusace ya jawo kujera ya zauna batare da ya jira anbasa iziniba suna fuskantar juna shida Alhj hisham. cikin gadara yake maganar sa,_

*Hisham wann shine karo na karshe idan har baka janye bakinka acikin maganar filin da ke k'auyen gurma ba wlh saika ga abinda ba dai2 ba zakayi da nasani akan taurin kanka dake cutarda kai,*

"Dakata honarable wann barazanar taku baxatasa na karaya na barku kucinye filayen marayu ba, ba filin gaunati bane hakk'in marayu nea bawani mahalu kinda zaisa nasa hannu don kucinma wata manufa taku dan haka kafita kabani guri yada yak'arasa maganr cike da tsawa.

_AFusace yamike ya kalli Alh hisham ya girgixa kai yanuna shi da yatsa niko? Yayi kyacci yafice daga office d'in afusace Excort d'inshi suka maramai baya_

 Bai shiga motarsa ba, saida yajima yana waya naso injiyo abinda yake fad'a amma badama inyo kusa dashi irin Yadda naga yad'au zafi yayima Excort d'insa hannu alamar sutafi.

Misalin karfe 4:00pm Alh Hashim yadawo gd ransa a6ace yashigo palour yasamu kujera ya zauna tare da kwa6e babbar rigar sa,

Wata mata tafito daga d'aki d'auke da cup d'in juice a hannunta  fara fess da ita tanufo inda yake ga alama itace matarsa,

"Alhj Lfy kuwa yana ganka ba kamar ynda nasaba ganin kaba'  "uhm bakmai fa Hajiya "ina *RAMLAT*  ya tambayeta

Shiru yabiyo baya kafin tace Ramlat tana d'aki tasa murya takirata amma itadai haryan xu hankalinta bai kwanta ba,

_Yarinya ce k'arama naga tafito daga d'aki cikin jajayen kaya kyakkyawa da ita ga gashin nan tamkar na indiyawa tanufo inda abban ta yake zaune cike da farin ciki da zuwa ta fad'a jikin sa ya d'ora hannun sa akan gashin kanta cike da so da qauna ba kowa bace wannan Illa_ *RAMLAT*

Anan ya dagota ya kalleta yayinda yaji wani tausayin ta yak'ara ratsashi bud'e bakinsa yace
"Yata kizamo mai girmama mutane kada kizalunci kowa idan mutum yasaka miki da sharri kibishi da Alkhairi kada ki wulak'anta kowa domin duk d'an Adam yanada baiwar da Allah yayi masa kuma aduk inda kika samu kanki kixamo mai taimakon Al'umma. Cikin maganrta ta yaranta tace

"Abbana zan iyayin duk abinda kace amma bazan taba d'aukar wulak'anci ba, murmushi yayi yace dakyau *RAMLAT* Allah yayi miki Albarka,

Ta kalli mamarta dake tace " mama kince idan Abba yadawo zamuje gidan tarihi d'auko mayafinki muje ba musu suka shirya suka fito suka shiga mota mai gadi ya bude kofa harza su fita ramlat tatuna da abin wasan ta wato babyn d'inta tace atsaya ta manta batazo da baby ba,

_Mama tace "keda zakije gidan tarihi mei zakiyi da baby acan kinga zauna yanxu baby nacan tana bacci kada kitasheta. 6ata rai tayi ganin haka Abba yayi reverse suka dawo tafito takoma gida ta d'auko babyn tana kawowa harabar gidan kamar antashi bom haka motar takama da wuta Abba da umma duk suna ciki.....))_

Tasaki babyn da ke hannun ta tanufi inda motar keci da wuta tana kiran Abbanta...!!!

Via OHW📱📚

🍀🍒🍀
              *RAMLAT"*
           _Yar Tsintuwa_
                          🍀🍒🍀

*_Written BY raheem jEgs📚_*

              🍒 _RaMlaT_ 🍒
                        *6_10*

_Iya Gaskiyarta tanufo inda motar keci da wuta tanakiran sunan Abban ta cikin murya mai karar gaske hawaye suka dararo a edonta tana kuka mai tsuma zuciya gata yarinya k'arama abin tausayi....))_

Jin sautin muryarta ne yasa 'yan dabar suka juyo da k'arfi sumar kansu ta yamutse fuskokin su rufe da wani bak'in mayafi banda edon su baka isa katsin kayi wata halitta ajikinsu ba, d'ai daga cikinsu ne wanda ga alama shine babba yaciko aguje yanufo *Ramlat* ganin tanufo inda wutar kecin iyayen ta, da zuwansa ya d'auketa da lafiyayyen mari saida ta had'iye kukan da takeyi tafad'a kasa tamkar anyi jifa da pure water ya d'auko bindigarsa yayi kicking yasaita bindigar dai_dai kanta sukayi edo 4 shida ita hannunsa yad'au rawa nan take yaji zufa takaryo masa duk jikinsa ya d'au rawa ajikinsa yaji wann yarinya Akwai wata baiwa a tattare da ita girgixa kansa yayi yamayar da bundigar aljihu yace "ku k'wamuso ta muje k'araminne daga cikinsu yace

"haba master miyassa zamu barta wannan fa mai wayoce ...duk saida tagama yiwa fuskokin mu kallo d'ai bayan daya, akanme zamubar ta,

Murmushi yayi kafin yace "Aa dan uwa mubar wannan yarinya atare damu domin nan zuwa gaba zatayi muna amfani musamman kaida kake gwauro suka kwashi dariya tare suna nunashi da yatsa.

_Suka fixgota tana kuka tana kiran Ummanta tana kallon motar naci da wuta daga nesa kana tsinkar gawar mahaifinta tana dukan bayansa akan yasauketa Amma kamr ba yajinta sai tafiyar mulki suke suna nuna isa, suna kai bakin gate alokacin taga gawar mai gadin gdn su wadda take kira da baban k'ofa, kwance acikin jini kallo d'ai zakayi masa kagane cewa bullet nea ya ratsa ta kansa,  wata JIB cea baka naga sunsaka ramlat suma sun tsunduma aciki duk tsegumina saida nayita lek'e2 Amma ban iya ganin mutumen da keciki zaune ba,_
     _bayan sun tayarda motar naga ya saukar da gilashin motar yazubar da yawu anan edona suka ganemun abin mamaki wazangani Honarable mukhtar wanda sukayi sa'insa da Alh hisham mahaifin ramlat acikin Ofishin sa,_

Gudu sukeyi cikin dajin Allah suka nufi wani mummunan daji dake cikin k'auyen Gurmu domin duk wata tsiya da'akeyi acikin YOBe a gurma ake tsulata,

Misalin karfe 10 na dare sukayi parking acikin dokar daji sukafito su duka sukabaro ramlat acikin motar kasan cewar barci yayi awon gaba da ita kud'i naga honarable yaciro ya damka'a musu haka dai suka jima suna shawarwarin su

_A mota kuwa Ashe ramlat ta farka tana kokarin bud'e kofar motar amma takasa abinka da k'aramar yarinya saifaman dukan glass takeyi azatonta murfin zaibude jikake gam gam da sauri sukanufo motar kasan cewar akwai tazara tsakanin su da motar cikin sa'a kafin suk'araso gambun motar ya bud'e tafado ak'asa tatashi takama tata hanya suka mara mata baya.....!!_

Gudu takeyi babu waige2 tanufi dajin Allah ita kanta batasan a ina take ba' gashi dajine mai hatsari cikin ikon Allah gudun da ramlat tayi koda babbr macece kokarin ta bazai wuce nan ba,
Koda ta isu bakin wani k'aton kogi taduba ko ina babu alamar hanya babu dama ta tsallaka wurin domin wurine mai ruwa da kuma manya duwatsa gashi da zurfin tsiya  anan taja burki gashi ta galabaita, juyowar da tayi ta hangesu da fitillu sunnufo inda take

 wasu kuyangar kara tagani dunk'ule kamar gije haka yarinyar nan ta kutsa aciki tasa hannu tatoshe bakinta tana k'watar numfashi tazare fararen edon nan nata tana kallon su kamar tasake da kuka koda suka k'araso wurin suka nemeta suka rasa, amma ita tana ganin su

Sunjima a wurin suna neman ta, amma wayam babban ne daga cikinsu ya taka hannunta da manya takalminsa batare da yasani ba amma haka ramlat tajure kuma tanajin zafi jikinta ya kwashi rawa harta sake da fitsari da xafin yayi mata yawa takasa hak'uri saita kaimasa zazzafan cizo asaman kafar sa yayi ihu yaciro k'afar  yana fad'in kunama tacijesa

*Ganin hakan tafito tanufi kogin da nufin fad'awa da sauri domin babu wata hanya mafi sauk'i a wurinta inba nan ta nuyo ta kalle su saida tak'are musu lallo kana tajuya tanufi kogin da nufin fad'awa ganin hakan honarable ya kar6i bundiga yayi saitin ramlat* _"kitsaya nacee yafad'a cikin tsawa_

*Amma ina yaro baisan mutuwa ba hakan baisa *ramlat* *tatsaya ba kukan harbi kakeji damm bullet yasauka ajikin ramlat tafad'a cikin katon kogi mai cike da manyan duwatsu...!!*

Via OHW📚

🍀🍒🍀
              *RAMLAT"*
           _Yar Tsintuwa_
                          🍀🍒🍀

*_Written BY raheem jEga_*

              🍒 _RaMlaT_ 🍒
                        *11_15*

*_ A K'AUYEN GURMA_*
_Washe gari misalin k'arfe 7:00am Al'adar garin ce sukan fito maza da mata domin zuwa d'ibar ruwa a babban KOGIN da ya ratso tacikin wanan k'auyen nasu mutanen k'auyen sun kasance suna bautar wani abu wanda ba Allah ba Sun kasance tamkar bayi haka ake mulkinsu cikin k'azamtacciyar rayuwa musamman ma 'yaya mata da aka mayar tamkar dabbo acikin garin_

*Al'adunsu kaff irin na musulmi ne Amma idan kazauna acikin su baxaka kirasu da musulmai ba,*

Matashin saurayi ne kyakkyawa dashi durk'ushi abakin kogin ya tara tulunsa da nufin d'ibar ruwa sai alamar jini yagani biye da ruwan hakan yasa ya d'auke tulunsa da sauri yakai duban sa a inda ruwan suke fitowa caraf edonsa yafad'a akan wani abu dake zuwa cikin jajayen kaya haka ya d'ora edon sa akan abinda ke zuwa ko k'iftawa babu kyakkyawar yarinya yagani fara fess da ita cikin rauni wasu sassa najikinta na fitarda jini bak'aramar razana yayi ba alokacin da edonsa yayi tozali da fuskar wannan kyakkyawr yarinya Amma yayi jarumta ya tsamota acikin ruwa ya rungumeta zuwa jikinsa Alokacin tayi ajiyar zuciya batara data k'arayin wani numfashi ba,

_Ganin haka yaciro mayafinda yake kansa ya rufe mata fuska dashi domin yasan irin hatsarinda zaishiga idan Aka kamasa da irin wann kyakkyawar yarinya a hannun sa, baijira komaiba darect gida ya nufa cikin ikon Allah harya isa gida batare da wani yasan abinda yake faruwa ba,_

Gida ne k'arami na itace tamkar na 'yan china wanda dagashi sai ummar sa da kuma qanwarsa humrat suke zaune aciki da shigarsa yajiyeta akan wani gadon kara wanda ko mashinfid'in kirki bashida kana yad'auko ruwa tare da wani farin kyalle ya goge duk jininda yake jikinta yacire kayan da ke jikinta da suka 6ace da jini ananne yaga Alamun harbi ajikinta da sauri ya d'auko Allura tare da wani k'arfe guda 2 masu tsinin gaske yaciro bullet d'inda yake jikinta hka dai yacigaba da bata taimako daga k'arshe ya shafe mata jikinta da magani a inda takeda raunuka harya k'arasa shiryata batare data farka ba, tsaye yayi akanta ya game hannayen sa yana rok'ammata sauk'i a wurin uban gijinsa, Ashe duk wann abin dayake qanwar sa humrat na tsaye tana kallon sa,...!!

*Hawaye sukayo chaaa a edon ta ta fad'a jikinsa tana kuka cike da tausayin wann k'aramar yarinya dake cikin wann yanayi sunjima a haka yana bubbuga bayan ta sannan ya d'ago ta yaja hannuta suka nufi inda ummar su.............))*

_Ya kwashe lbrn duk abinda ya faru yabasu tundaga lokacin da ya tsinto ta har izuwa yanxu, suka tashi suka nufi d'akinda take kwance har Alokacin bata farka ba, tun alokcin da edon umma yayi tozali akan wannan yarinya taji ajikinta cewa zaman wann yarinya atare dasu babbar matsala ce agarsu girgixa kai tayi ta kalle sa canxa fuska tace tace_

*"Ashraf* Ni mahaifiyar kace na umurce ka dakayi gaggawar fitarda wann yarinya acikin gidannan "yakake tunanin rayuwar mu zata kasance idan shugaba murtu yasan da zaman wann yarinya a gidannan? Wane irin hukunci kake zaton abin bauta zayyan ke muna idan yagane cewa muna 6uyar wani mutum batare da mun bayyanar dashi ba,

*wannan yarinya ba jininmu bace abin bauta yatsaneta* kayi gaggawar mayarda ita a inda kad'auko ta abin bauta yatsane ta, Afusace tabaro d'akin yayin da Ashraf ya fashe da kuka idan ya kalli yarinyar sai yaji tausayinta ya ratsashi yaji baya iya rabuwa da ita,

_Yaje ya samu mahaifiyar sa, ya durk'usa ya kama k'afarta "ummata ina rok'onki daki bari muzauna da wann yarinya atare damu kidubi irin raunukan da suke jikinta, a wane irin hali tafito bakisani ba, yazakiji idan daya daga cikin 'yayanki suka tsinci kansa acikin irin wannan hali, abin bauta zayyi alfahari damu idan muka ceto rayuwar wannan yarinya....!!_

*Ninajiya ajikina wann yarinya Akwai baiwarda ketare da ita, yak'arasa maganr cikin kuka wani irin tausayinsa yakamata ta dafa kansa tace "Shikenan d'ana na aminta kaci gaba da kulata Abin bauta ya albarka ceka wani irin dad'i ya ziyarci zuciyarsa murmushi yayi ya rungumeta yace "Jinjina ga abin bauta.....))*

        *BAYAN KWANA BIYU*

Zaune suke a cikin wani Lambu mai sanyi da kuma k'amshin gaske ga wasu manya jarumai a zagaye dasu dagani kasan su 'yayan gidan sarauta ne shiru kakeji na tsawon Lokaci batare da kowa yayi magana acikinsu ba, Alamun suna cikin zafin zuciya bud'e bakinta tace

_"Ashraf a yanxu kacanxa narasa mei yake damunka nea hatta da wurin bauta kadaina zuwa kuma a haka kake zaton Zamu samu Albarkar aure a wurinsa, "waime yake damunka nea Ashraf? tak'arasa maganr cikin b'acin rai,_

Ya d'ago kai ya kalleta yace "bahaka bane *HAYBA* na rantse da abin bauta ina sonki kuma zan aure ki Amma a yanxu Akwai abinda yake gabana wanda nikaina banada Lokacin kaina balle nawasu "Amma....^ kafin yak'arasa yaji muryar qanwarsa Humrat..!!
    "Ya Ashraf kazo da sauri *'Yar Tsintuwa* ta farka wani zare edo yayi ta farka ya maimaita abakinsa cike da farin ciki ya mik'e da sauri yace

"I'm sorry *HAYBA* pls zanje gida saimun sake had'uwa baijira tayi magana ba, ya zarce da guda yanufi gida cike da mamaki tace "Yar tsintuwa Waye ita wlh Ashraf baka isaba ta fixgi takobin da ke hannun dai daga cikin Fadawanta ta  tabi bayan *Ashraf* A fusace....!!

Via OHW📱📚

🍀🍒🍀
              *RAMLAT"*
           _Yar Tsintuwa_
                          🍀🍒🍀

*_Written BY raheem jEga📚_*

              🍒 _RaMlaT_ 🍒
                        *21_26*

_Tsaye take tana kallon k'ofar gidan cike da tausayi a lokacin tunanin iyayenta ya fad'o mata arai tatuna irin yanda take samun gata da cikakkakiyar kulawa a wurin Abban ta fashewa da kuka saida tayi mai isarta edo sun mata jajir gatq a tsaye tana kallon gdn Amma mahaifiyar Ashraf tayimata iyaka dashi, tajima a tsaye canta canxa fuska kawai ta kutsa kai takoma Acikin gidan taje inda umma taja birki tagame hannayen ta 2 tanaba ta hkr kamar yanda taga sunayi idan suna  bautar su,_

A fusace umma tad'aga hannu sama danufin wanketa da mari caraf humrat ta rik'e mata hannu tace
   "haba umma idan kikayi haka kinzubar da darajar ki awurin abin bauta, yau kusan kwana 10 da zuwan 'yar tsintuwa a gidannan amma batataba cutar muba hasalima sai soyayya ke k'ara shiga tsakanin mu da ita meyasa zaki koreta umma? Mei tayi mikine kike mata wann tsana to wlh idan harkikace dole saita bar gidan nan tonima zanbita domin nasan nata iyayen baza su hanani zama atare da suba,

_umma ta fixgi hannun ta daga hannun 'yarta humrat tayi kyaci tawuce abinta, wani dad'i Ashraf yaji rungume 'yar tsintuwa yayi yana ta shafar kanta itama tasa hannu tana share hawayen da ke zuba a edonsa kasan cewar lokacin darene ya d'auketa zuwa d'akinta ya shimfid'eta kafin yatafi yajima yana mata tambayoyi Amma har a lokacin bata bud"e baki tayimai magaba ba, saidai ta girgixa kai Alamar eh ko aa, tashi yayi danufin tafiyar sa tabata rai kamar zatayi kuka hakan yasa yaje yad'auko kayan barcinsa, yaxo suka  kwanta tare,_

Misalin karfe 2:30pm na dare 'Yar tsintuwa ta farka a hankali ta zame jiki taje ta bud'e kofar d'akin  tafita batare da Ashraf ya farka ba, sannan ta rufe k'ofar a hankali take tako d'ai bayan daya harta sace jiki tafita daga gidan batare da daya daga cikin su ya farka ba, cikin tsalelen dare gashi ba wuta banda kukan karnu ka ba abinda kakeji haka takama hanya saikace Aljana tanufi gidan shugaba, murtu Acikin tsalelen dare Abin mamaki mei ya fidda ta Acikin wannan dare kuma mei zatajeyi a gidan shugaba, murtu a wannan lokaci sarkin da kowa yake matuk'ar tsoron sa,

Harta isa gidan sarautar bataci karo da kowa akan hanya ba, Amma zuwanta kofar gidan ta taradda k'attinan jarumai sai zagayen gidan suke wasu da takubba wad'ansu da bindigogi a hannayen su wasu kuma a saman gidan sunyi tsaye kamar guma ka,

 Babu tsoro kokad'an ajikinta tawuce kai tsaye bata tsaya ko inaba sai bakin gate d'inshiga Acikin wann babban gida na sarauta wani sai a lokacin wani k'aton mutun bak'i kakkaura a k'alla zaikai girman mutum 3 tundaga nesa ya hango ta cikin jajayen kaya bak'aramar razana yayiba,  da sauri ya zaro takobinsa ya haskota da wata irin touch light mai haske yace.....

"Tsaya daga nan ke wacece mutum ko Aljan? tayi kamar batajishi ba, sai k'ara yowa cikinsa take jikinsa ya da'au rawa ya kamaja da baya abin dariya yabata ganin haka hankalin sa yak'ara tashi yayi ihu ya bud'e gate d'in da sauri nan take kaga fadawa sunfito d'auke da makamai azaton su farmaki nea aka kawo musu

Ganin fitowar su A saman dawakai tad'anji tsoro tabuya a k'arkashin wani tebur harsuka gama fitowa fitowa tayi da gudu tanufi cikin gidan batare da wani yaga wuce warta ba, tafad'a cikin wann gida na sarauta duk wann abin da'akeyi haryan xu kowa yakasa fahimtar abinda ke faruwa,

 Wani d'aki tanufa wanda aka k'awatashi da kayan ado irin na sarauta ta kutsa kai aciki caraf edon ta suka fad'a kansa tayi ajiyar zuciya tabbas shine wadda tagani a gidan su Ashraf kuma shine jagaron wad'anda suka kashe mata iyaye,

kwance yake saman wani Lafiyayyen gado sai kwasar barcinsa, yakeyi tayi murmushi ta mayarda k'ofar d'akin tarufe ta janyo wata igiya dake kasan gadon tad'aure masa kafafu kana ta kama hannayen sa, ta d'aure batare da ya farka ba tacire k'yallen da ke rataye a kafad'ar ta ta rufe masa baki ananne ya farka Azuci take fad'an "yau kwanan ka yak'are kaima zaka d'andani Azabar mutuwa kamar yanda kuka rabani da iyayena, firgigit yatashi kamar wanda aka cema tashi za'akashe ka ya k'ureta da kallo tabbas yatuna wann fuskar da karfi yayi yunk'urin tashi yaji jikinsa a d'aure dariya tayi tafidda wata sharb'ebiyar wuk'a ajikinta duk inda tasamu soka masa takeyi fuskarta duk jinine hakama hannayen ta bata bariba saida taga yadaina numfashi,

_A wurin Ashraf kuwa mummunan mafarkine yayi ankashe 'yar tsintuwa firgigit ya farka ya lalubo ta, ko sama ko k'asa babu yar tsintuwa yashiga kiran sunanta yana dube dube hankalin sa, yatashi yatada humrat ya tambaye ta "ina 'Yar tsintuwa ? Tace niban ganta ba, "ina tashigane.    suka fito waje suna kiran sunanta Amma shiru kakeji nan hankalin su yayi matuk'ar tashi yakama hanya baimasan inda zashiba, sai faman kiran sunanta yake shikad'ai Acikin dare.......))_

Nan humrat ta fashe da kuka tace "ya Ashraf dan Allah kadawo kada Azzalumannan sukama ka, nasan bazasu barka da raiba,  Ashraf baima san tanayi ba saik'ara kutsawa yakeyi cikin duhu

*Sunci bid'a harsun gaji suka dawo gida suka jawo kofa suka rufe suna juyowa kwatsam suka ganta a tsaye jikinta duk jinine sai murmushi tana d'aga musu hannu. tana kallon su gabaki d'aya tsoro ya kamasu cikin rawar murya Ashraf yace 'Yar tsintuwa Nine Ashraf kece kuwa....??*

Via OHW📱📚

🍀🍒🍀
               *RAMLAT*
           _Yar Tsintuwa_
                           🍀🍒🍀

*_Written BY raheem jEga📚_*

             _🍒RaMlaT🍒_
                     *26_30*

_Ta girgixa masa kai k'arasawa yayi kusa da ita cikin tsoro ya d'ora hannun sa, a kafad'arta ya zame rigarda ke jikinta nan yaga tambo ajikinta hakan ya tabbatar mai dacewa itace Amma mei ya fidda ita acikin wannan dare kuma a ina tagamu da wannan jinin dake jikinta, wann itace tambayrda yakema kansa. Humrat tadafa ta tace "k'anwata daga ina kike ? Kuma waye yabata miki jiki da jini haka? tasoke kai k'asa batace da ita k'alaba, durk'usawa humrat tayi ta rik'e hannuwanta 2 tace "Nasan keba kurma bace SBD kinajin abinda muke fad'a dan Allah kigaya muna wacece ke.....?_

Nan tasake da hawaye ta fara kuka ta kw'ace hannunta taje inda Ashraf ta rungume sa, tana kuka zame jikinsa yayi ya zaunar da ita, ya dubeta yace "Yar tsintuwa ta Nasan bazaki b'oyemin komaiba kifad'amin kinkashe wanine a cikin darennan ? Ta girgixa masa Alamar Aa....yayi ajiyar zuciya yace to "A ina kika samu wann jinin tanuna masa k'ofar fita da yatsa Amma shi haryanxu baigane abinda take nufiba, yace Ni banga kowa ba, k'anwata "kinyi Alqawarin da safe zaki kaini inda kikaje a cikin wann dare ta d'aga kai Alamar ehh....!!
     *Baik'ara tambyr ta komaiba humrat tajata taje da ita tayi mata wanka ta canxa mata kaya tajata zuwa dakinta suka kwana tare har garin Allah yawaye*

Yau takama Ranar Laraba, ranace babba agaresu maza da mata kowa yana fitowa zuwa wurin bauta kamar yanda suka saba kuma ranace da kowa yakeyin abinda yakeso batare da takuraba, wad'ansu susha kayan maye kuma suna zuwa wurin wasanni a gidan SARKI MURTu a ranar cea duk wani Namije yanada damar yayi Amfani da duk wata mace da yakeso dake cikin gariN GURMA,

 _A wurin su Ashraf kuwa suma sunyi Nasu shiri cikin fararen kaya Massamn Ashraf yaci kwalliya irin yanda yasaba, doguwar riga da wando white yad'auko rufaffen takalminsa suma farare yasaka kana yad'auko wani farin mayafi yarataya a kafad'arsa ga sumar kansa ta kwanta luf_luf _haka ma a wurin umma da humrat nd 'Yar tsintuwa duk cikin fararen kaya suke k'amshin turare kawai kakeji suka fito suka zuwa babbar mujami'arsu da take a k'ofar gidan shugaba Murtu,_

Da zuwan su Ashraf ya mik'awa humrat yar tsintuwa ya kutsa kai Acikin gidan SARKI murtu haka yasamu fadar Acike Amma bacikin yanayi mai dad'iba, Gawace yagani ajiye a tsakiyar fada mayafin 'Yar tsintuwa yagani Asaman gawar tabbas ba shakka wannan mayafinta nea Nan take hankalin sa yatashi sai rabon edo yakeyi Acikin fadar kamar marar gaisuwa cikin girmamawa yaje gaban sarki ya fad'i ya kwashi gaisuwa sannan ya gaida umman HAYBA da sauran manyan da suke wurin, zaune ya hango HAYBA tana masa murmushi SBD taji dad'in ganinsa hannu shima ya daga mata baik'ara kallonta ba sbd kunyar surukan sa da yakeji, a hankali sarki yake tako yana wuce mutanen da ke tsaye acikin fadar saida yakawo wurin Ashar yatsaya ciff yadafa kafad'ar sa, bud'e bakin Yace

"Ashraf a yanzu kaine jaruminda nake ganin zai iya rik'e ragamar wannan masarauta tamu kuma haka nake ganinka tamkar d'anda na haifa Nasan bazaka bari Aci mutunci wannan masarauta tamuba, yanuna gawar da yatsa kafin yace "wannan itace gawar babban jarumin wannan masarauta a daren jiyane a kayimasa kisan gilla kuma yazama dole kanemo maccen da takeda wannan mayafi Acikin garinna,
      Domin itace takasheshi....!! da sauri Ashraf ya d'ago kai Azuce yace 'Yanxu anan 'yar tsintuwa takasheshi jikinsa yad'au rawa murya k'asa yace angama ranka yadad'e

Aka dauki gawar SARKI nea a gaba Al'ummar sa nabiye dashi suka fito zuwa wurin bauta HAYBA kuwa cike da farin ciki tarungume hannun Ashraf suna tafe sai murmushi take masa Amma kaff hankalinsa baya garesa, tunanin 'YAR TSINTUWAr sa, yakeyi shifa haryanxu baiyarda cewa itace tayi wannan babban kisan ba,

A bangaren su umma da humrat sun duk'ufa wurin bautar gunkin su yar tsintuwa na rungume a hannun humrat yayinda sarki da mutanen sa suka fito mutanen garin suka kwashi ihu ana Ambatar sunan sa, Amma a lokacin ransa abace gaba daya hankalinsa baya gareshi can edonsa suka fad'a akan kyakkyawar yarinyar dake rungume a hannun *humrat* d'arrr yaji abu azuciyarsa yayinda ya kifeta da kallo a lokacin da yaga tana k'okarin fixge jikinta tana nuna mayafinda ke saman gawar tana dukan bayan humrat, Azuci yace tabbas mahaifiyar waccan yarinya itace keda wannan mayafin d'aga murya yayi yace "kuzomin da waccan matar dake d'auke da yarinya..!!

Juyowar da humrat tayi sai k'atti tagani sunnufo ta da gudu tak'ara k'akkame 'yar tsintuwa ajikinta tarutsa cikin taro tana gudu haka suma suka biyota.....da adduna a hannun su,

*Acan wurin su Ashraf HAYBA tad'auke masa hankali tajashi zuwa cikin wani k'aton holl inda babanta yake tasa bauta shikad'ai idan yatashi wurine Lafiyayye Ank'awatashi da kayan ado na sarauta tasa Aka kawo musu kayan ciye_ciye dana sanyi aciki harda barasa,*

Suna fira suna ciye ciye HAYBA tana matuk'ar sOn Ashraf sun kusan 2 hours Suna fira gabaki daya tayiwa wani narkewa ajikinsa yasa hannu ya rungume ta zuwa jikinsa hakan yasa yamanta da halinda ya baro qanwarsa dake tare da Yar tsintuwa domin yasan komai zai iya faruwa idan taga wannan mayafin Nata, dake kan wann gawar "Ohh Yar tsintuwa ta, yafad'a da sauri yature HAYBA dake kwance a jikinsa yatashi daanufi yaje inda qanwarsa caraf yaji anrike masa riga "No Ashraf ba inda zakaje waikai mei yake damun kane Na fahimci ko kad'an bakason fira dani
       dafa kafad'arta yayi yace "i'm HAYBA wlh ba hakabane i'm really luv u na rak'eki kibarni natafi Akwai matsala wlh tafashe da kuka tasake masa riga tajuya tayi cikin wani d'aki dake wurin haka shima ya juya yanufi mujami'a

_mamaki ya kama ta ranta yayi matuk'ar baci wannan shine karo na2 kenan tO wlh yau nida kaina zanje inkashe wannan_ *'Yar tsintuwar* tafad'a yayinda zuciyarta take cikin zafi

Via OHW📲📚

🍀🍒🍀
               *RAMLAT*
           _Yar Tsintuwa_
                           🍀🍒🍀

*_Written BY raheem jEga📚_*

             _🍒RaMlaT🍒_
                     *31_36*

```Haka Ashraf yake ratsa mutane kasan cewar jama'a sunyi yawa a wurin hakan yasa yajima baikai inda yabaro qanwarsa ba, jiyaye anbangaje saura kad'an yakai kasa A fusace yataso ya daga hannu da nufin kai bugu sai k'atti ya gani d'auke da takubba a hannun su, "sukuma wad'adannan wasuke nema nea ? Yafad'a azuci k'anwarsa yagani rungume da Yar tsintuwa sai gumi take tana waige2 hakan ya tabbatar mai da cewa tabbas ita suke nema,```

_A lokacin yakira sunanta muryarsa data jiyo tawaigo da k'arfi tace *"ASHRAFF*  kamar tasake da kuka kasan cewar ta galabaita wani irin k'arfi yataso masa yashiga bangaje mutane yana gudu itama a wurinta gudun takeyi haka suma k'attin basu daina bibiyanta ba, kasan cewar ba hanya d'aya sukabiba Ashraf ya rigasu kai da zuwansa ya k'arb,i 'Yar tsintuwa hannunta yayi tsaye cakk a wuri d'aya cike da tsoro tace "ya Ashraf dan Allah mugudu tanajan hannunsa tana fad'in kazo mugudu ya Ashraf yadaka mata tsawa "NO Humrat kigudu nace....))_

Ganin yadda suka tunkaro inda suke hakan yasa ta face da gudu tanufi mujami'a inda umma take tafaman sambad'a bauta kamar mai shirin kuka tadafa umma tace "umma dan Allah mubar wurinnan nifa inajin tsoro "Aa humrat abin bauta yasan damu ba abinda zaifaru umma tafad'a sai wani waige2 humrat takeyi tazo gaban umma takama hannunta tace "pls umma kizo muje gida Akwai matsala umma dan Allah kizo muje pls umma ganin haka umma tabita suka kama hanya saure kawai suke suka nufi gida,

*A wurin Ashraf kuwa yanacan yana fafatawa da yaran gidan Shugaba murtu yayinda suka sanardashi Sarki yabasu izinin suzo da wannan yarinya Amma yace ba inda zasuje da ita kawai suka haushi da fad'a sunata kawo masa sara yana kaucewa saifamar maxgarsu yake duda hakan 'yar tsintuwa narike a dayan hannunsa, sannu sannu duk saidai yaga bayansu Amma sunyimai raunuku dadama dakyarr ya iyakai kansa gida,*

Tafe suka hangoshi d'auke da ita a bayansa Amma farar rigarsa bata kalluwa SBD tayi kaca kaca da jini da gudu humrat taxo ta rungumesa tafashe da kuka umma tazare edo tafara shirin hawaye tace "d'ana mei yasameka inace basanadin wannan muguwar yarinyar akayima wannan raununkan ba, ya girgixa kai Amma umma bata yarda ba taciyo kwalar ta tace kee dan ubanki banhanaki shigowa gidanna ba? da sauri ya daga hannu ya girgixa wa umma kai sannan tasaketa mik'ewa tsaye yayi ya kalleta Afusace yace "Wacece kee?

_Sai A lokacin tatabajin Ashraf ya mata magana cikin fushi sunkuyar da kanta k'asa tayi Alokacin shine na farko da suka farajin muryarta yayinda tace_

```"sunana RAMLAT Kumani yar garin YOBE cea Amma nayi kuskure daban sanarda ku koni waye ba bana son tuna baya shiyasa bansanar daku tarihina ba, ta d'ago kai ta kalli humrat tace "zanbar muku gidan ku nima banajin dad'in ina sakaku acikin matsala Amma kobayan wasu shekara zandawo bazan iya mantawa dakuba, Hawaye sukawo shaa a edon Ashraf ya d'aga hannu zaikira ta Akan tadawo umma tace "Aa d'ana kabarta tatafi ko a yanxu batagama kisan ba, humrat tafashe da kuka "Aa umma inason Ramlat dan Allah kada kibari tatafi....!! Haka umma tacije Ramlat takama hanya tabar gidan batasan inda zata dosaba, gashi kuma agari sai faman nemanta Akey```

A ranar haka Ashraf yayini jiki sakaka humrar ma duk taji badad'i an rabata da 'yar uwarta Allah kad'ai yasan enda Ramlat take a Yanxu,_

Labari yasauka a kunnen SARKi yajima yana kai kawo a cikin fada cike da mamakin Ashraf Azuciyar sa kuma tunanine k'arara a yanxu wane irin hukunci yadace da Ashraf dagashi har k'anwarsa, Abinda yaba mutane mamaki Tunda SARKI yasamu wann lbrn baik'ara yiwa kowa magana ba, jama'a sun k'agu suji abinda zaifito daga bakin sarki, Amma shiru kakaje baima kowa mgn ba, har dare yatsala babu wani imformation,

Misalin karfe 12:45Am na dare iska sanyi yafara k'adawa Ashraf dai barci yaga gareshi Yataso ya d'auko bargon da yake rufe dashi kana yaje a bakin window yayi tsaye yana kallon farin wata dayayi fari fess yajima. a haka sannan yasa hannu zaijawo tagar kwatsam yaga mutum zaune rik'e da tufafi a hunnunsa sanyi na dukan jikinsa yana karkarwa,

Fitowa yayi danganin kowaye Abin mamaki sai *RAMLAT* yagani batamasan da zuwan sa ba, cikin mamaki yakira sunanta RAMLAT...!!

```A tsorace tadago kai ta kallesa, Cikin muryar yaranta tace "ASHRAF yace "Na'am.   Me yadawo dake....?```

Via OHW📲📚

🍀🍒🍀
               *RAMLAT*
           _Yar Tsintuwa_
                           🍀🍒🍀

*_Written BY raheem jEga📚_*

             _🍒RaMlaT🍒_
                     *36_40*

_Jin muryar sa, da tayi ta d'ago kai a tsorace tace "ASHRAF yace "Na am ralmat mei kikeyi anan? Ya tambeta shiru tayi ba amsa jikinta sai rawa yake kasan cewar sanyin da yake' sauka a lokacin tausayinta yakamashi ya rik'a hannuta da nufin yajata sushiga cikin gida tak'ara mak'alewa ta girgixa kai tace "Aa ya Ashraf dan Allah kabarni anan idan nashiga umma zatakasheni,_

```Yace "aa ramlat bazan barki anan ba, kizomuje ciki nasan yanxu umma tayi barci, ya lallasheta harya samu tabishi har Alokacin rungume take da wasu uniform na yara a hannunta ko a ina tasamo uniform d'in Allah masani, yajata zuwa d'akinsa ya azata kan gado yad'auko bargo yarufe mata jikinta nan take barci ya saceta wani daddad'an mafarki yaziyarce ta gata tana rayuwa tare da iyayenta kamar abaya dad d'intane yake mata wasa tana dariya cikin annashuwa, katsewar mafarkin nata shiya tada ita tatashi zaune tayi shiru tana tunani mafarkin da tayi hawaye ne suka biyo baya  hannu tasa tana jijjiga Ashraf Amma ina yayi nisa Acikin barcin da yake taga bayada niyar tashi tasauko Ak'asa jikinta na kaekarwa sanyi nashiga jikinta ta d'auki tufafin da tazo dasu Alokacin dai dai hasken wata yafara fitowa tabud'e k'yauren gidan tafito takama hanya batare da Ashraf ya farka ba,```

Washe gari da ya farka yanemi Ramlat ba ita ba alamar ta, Al'amarin da yad'aure masa kai kenan Shidai haka yake ganin Abin kamar mafarkine ba gsky bane, kuma baisanar da kowa ba, shiru yayi yana tunanin faruwar wann Al'amarin zuciyar sa tafara raya masa cewa ramlat Aljana cea, yana cikin haka yajiyo kukan dawa kai tafe kamar zasu shigo acikin gidan jiyayi an shuro gambun gidan 'kattine guda uku suka ratso da dawa kai Acikin gidan sukaja birki ciff agabansa, d'ai daga cikinsu yayo ta kansa yatakashi da doki 🏇 ya fad'i k'asa kujerar da yake zaune akanta ta kare suka sashi tsakiya sai faman dukanshi sukeyi jikinsa yayi jinajina da gudu hayaniyar da tayi yawa shiyafito da humrat  tayo kansa tana kiran sunan sa, ta fad'a jikinsa ta k'ank'ameshi tana kuka suka sauko akan dawakan suka k'waceshi daga jikinta saukar lafiyayyen mari taji a fuskarta, saida tafad'i k'asa

_Umma kuwa k'arar marinda akawa humrat yafito da ita da fitowar ta edon ta suka fad'a akan Ashraf  k'asa kwance tasaki plate d'inda ke hannunta tayo kanshi tafad'i k'asa tana jijjigashi tana kiran sunanshi cikin murya kuka._
        *"takama kiran wayyo Allah sun kashemun da'ana Ashraf katashi karka mutu dan Allah ko sauraren ta basuyi ba, suka d'auketa da k'arfin tsiya suka dorashi Akan doki suka kama hanya darect sai gidan SARKI MURTU,*

Har alokacin humrat kwance take bakinta na fidda jini umma ma haka sai faman kuka sukeyi suna sambatu,

A tsakiyar fadar suka saukeshi a fusace sarki yaxo yad'ago kansa,ya tofa masa yawu yace "tirr da halinka wlh kuma abin bauta yana fushi dakai, da ina d'aukarka tamkar d'ana ina ganin kaine zaka maida martabar wann gidan Ashe dakai ake k'okarin kashemin jarumai, kafad'amin a ina kab'oye wannan yarinya kuma wacece ita,? sai yawun jini kawai ke fita abakinsa baisamu damar bashi Amsa ba, Sarki yace "Ashraf yazama dole na hukunta ka dai dai da abinda ka Aikata, ya dubi fadawan da sukazo dashi yace "kuje dashi ku masa dukan tsiya harsai ya fad'a muku inda yarinyar take, d'ago kai Ashraf yayi ya kalli HAYBA da take tsaye ta kauda kanta da sauri duk da raunu kanda suke jikinsa Amma ta kanne tabarshi aka tafi dashi suna fita tafashe da kuka ta fad'a jikin mahaifiyarta,

```A wurin Ramlat kuwa bayan fitarta daga gidan su, Ashraf tazo k'arkashin wata bishiya tayi kwanciyarta misalin k'arfe 7:00am tacire kayan da ke jikinta ta saka wann unifm dake hannun ta tashirya kaff takama hanya yara ragani k'ana sanye da uniform irin nata tabi sahunsa idan ka ganta baxaka banbanta ta da d'aliban makarantar ba,```

_Sunkusa isa makarantar ta hangowa wata tsohuwa rik'e da jikinta a tsaye jikan nata sai kuka yake da sauri ramlat ta kutsa cikin mutane domin uniform d'in yaronne tasace tasaka'  hartaxo ta wuce tsohuwar batare da taganta ba,_

Makarantar yarace maza/mata k'anana wadanda bazasu haura sama ga shekara 10 ba, haka take rabon edo acikin makarantar batasan kowa ba, bayan angama Asembly kowa ya wuce class d'insu tsaye tayi domin batasan class d'inda zataje ba dama ita bakaratun yakawo ta ba, tunda aka fara Asembly take kallon sa, har aka gama edonta na kansa, bayan yashiga Office d'insa tabishi a baya suku suku sai cikin Office, da zuwa tayi sallama ya Amasa batare da ya dago kai ya kalleta ba, sai rubuce rubucen sa, yakeyi shiru tayi batace k'alaba saida yagama rubutunsa A fusace ya d'ago kai yace "wacece ke dazakizo office d'ina kimun shiru me kikazoyi ?
    Sai Alokacin tad'ago kanta ta kalleshi sukayi edo hudu da juna damm gabansa ya fad'i yace "kee dama baki mutuba, wayakawo ki wannan makarantar ? tace "shayine wata malama tace inkawo ma gashi a cupy a tsorace yazura hannun sa zaikarb'a jiyayi ta watsamai ruwan ACID ajiki kafin yamik'e tasake zubamai ruwan Afuska ya saki ihu yasulale a k'asa gashi ba kowa a lokacin ballai akawomai agaji tana gani haka tajuya da sauri tabar Office d'in

 _A bakin k'ofar fita daga office d'in dai2 da shigowar wata malama sukaci karo da juna saida ramlat ta fad'i k'asa da sauri malamar tatada ita tace "sannu ko...!! Kallonta kawai ramlat tayi tawuce tana sauri tabar makarantar,_

*Da shigar malamar Acikin office edon ta suka fad'a akan principal d'in makarantar wani irin jiri ya kamata yayinda taga fatar edonsa duk ta d'aye*

 ```Da gudu tabaro Office tafito tana ihu nan take sauran malamai sukayo kanta d'alibai suka firfito da kowa ya fahimci abinda ke faruwa yara sai guduwa suke sunayi gida Ramlat kuwa tuni tajima dayin nisa mota tagani anyi parking ga Alamu pasinger ake jira da zuwa tafad'a Aciki ta samu kujera tazauna kowa sai kallonta yakeyi hakan yatayar mata da hankali jikinta ya d'au rawa sai wani rabon edo take tana kallon mutane.....))```

🍀🍒🍀
               *RAMLAT*
           _Yar Tsintuwa_
                           🍀🍒🍀

*_Written BY raheem jEga📚_*

             _🍒RaMlaT🍒_
                     *41_46*

_Zaune take cikin motar Amma har Alokacin hankalinta ba kwance yake ba, gane take kamar yanxu kamata za'ayi kallo d'aya zakai mata kagane Alamun marar gsky ce, wata matace dake kusa da ita ta fahimci halinda take ciki ramlat ta k'urawa matar edo duk lokacnda matar tajuyo sai ramlat ta kauda kanta da sauri haka suka sukewa junansu kallon tuhuma, har motar tacika driver yatada motar suka wuce_

A can makarantar kuwa komai yarikice d'alibai sai firfitowa suke sunayi gida, Al'amarinda yad'aurewa malaman makarantr kai kenan wayayi wann mummunan kisa? Itace tambayr da sukewa junansu, malamr cea talabar ta musu abinda duk yafaru a tun dga farkon had'uwarta da ramlat a lokacin da zatashiga office d'in yanayinda taga yarinyar a lokacn tabbas bana masu gsky bane, wasa_wasa Al'amari yayi nisa Labari ya watsu agari har a gidan SARKI,

Afusace yanufi wani kangon wuri inda aka ajiye Ashraf d'aure yake ajikin kujera yana cikin mummunan yanayi kasan cewar dukan da yasha  kujera aka azawa SARKI yazauna suna fuskantr juna shida Ashraf, hannu yasa yad'ago kansa shiru yayi yana masa wani kallo cike da gadara jiyake kamar yasa hannu ya shak'esa, murya k'asa yace "ASHRAF me yasa kazab'i mutuwar ka Akan rayuwar ka? Wannan yarinyar wacece ita....? Kuma me yasa take kashe mana mutane? Sarki yafad'a afusace Amma shiru kakeji babu amsa abakin Ashraf,
       _"Dakyau Nasan kobaka bani amsaba tozaka bada Amsa don wannan yanuna ta da yatsa, koda Ashraf ya d'ago kai wazai gani ((k'anwarsa humrat)) a daure cikin wani yanayi ana tunkud'ar k'eyarta da k'arfi aka turota tafad'i agabansa, da sauri Ashraf yace "Aa dan Allah kada mutab'amin k'anwata na yarda zangaya muku wacece_ ```"YAR TSINTUWA```

```Nan take ya kwashe lbrn ta kaff yagaya musu dga k'arshe yace "Kai babana ne kuma dole in sanarda kai bayaranka kad'aiba kaima nan zuwa Lokaci kad'an RAMLAT nanan zuwa kanka domin nasan bazata barka, inace kanada masaniya akan Alh Hamshi kuma kana d'ai dga cikin wadanda suka bada goyon bayan Akasheshi..))

Shiru Sarki yayi zuwa wani lokaci sannan yamik'e tsaye ya kalli fadawan sa, yace "kuci gaba da azab tardashi harsai yafad'a muku inda yarinyar take, humrat tafashe da kuka tafad'a jikin yayanta daky'ar suka cirota ajikinsa tan kuka tana fizge2 suka wuce da ita tana kallo ana dukansa da manyan itace_

*YOBE STATE*
```Bayan motar ta saukesu suka firfito kowa yad'au kayansa yak'ara gaba itama matar taje agefen titi tana jiran mai napep "Sannun ki Aunty da sauri tajuyo jin muryar da tayi. murmushi tayi kafin tace "wacece kee? Ramlat tace "d'iyar kice..!!  Matar tace "uhm bakiyi k'aryaba yarinya domn na haifeki, Amma wacece ke?```

Ramlat tace idn nafadamiki bazaki kasheni ba,? Dariya tayi kafin tace "banda abinki wace uwa zata kashe 'yarta akan tabata lbr,  wani shu'umin murmushi ramlat tayi kafin tace "Ni marainiya ce bnda kowa a yanxu saike nabiyo kine aunty sbd bnsan inda zanje ba, dn Allah kada kicutar dani namiki alqawarin idan mukaje gd zakiyi matuk'ar mamaki idan kikaji lbr na, shiru tayi tana kallon bakin ramlat "anya kuwa wann yarinya itace da kanta take wann mgrn ? tafad'a azuci kafin tace "Ohk zomuje gida "Amma ya sunanki tabata amsa "sunana Ramlat aunty hannun ta tarik'a suka tare napep darect sai unguwar sabon gari,

🍀🍒🍀
               *RAMLAT*
           _Yar Tsintuwa_
                           🍀🍒🍀

*_Written BY S.raheem jEga📚_*

             _🍒RaMlaT🍒_
                     *46_50*

       ```HAPPY JUMU'AT
        MUBARAK```
*I'm sorry my fans 2 dayx da kukajini shiru bisa wasu dalilai dasuka tsaidani bt yanxu in shaa Allah i'm Okayy zakujini Akoda yaushe thanks u all fans))*
                 👇🏻

_Da zuwan su gida matar tad'auko abinci da ruwa taba ramlat, dama yunwa takeji saida taci mai isarta tasha ruwa ta wanke hannu matar tace_

```"to ramlat kinga wann gidan duk nawane kuma nikad'ai nake a ciki nagadi gidan ne a wurin mahaifina da yarasu shekara 1 data gabata, mu biyu ne a wurin mahaifinmu dagani sai yaya umar wanda ankashe shine sanadiyar ceton Abban mu dayajeyi a lokacinda 'yan adawa suka kawo masa farmaki don kawai suna son su mallaki wani babban filinsa, dake cikin k'auyen gurma.```

_Sunkashe min Abbana da yaya umar mahaifiyata kuma tarasu ne sanadiyar hawan jinin da takamu dashi bayan mutuwar Abbana wannan dalilin ne yasa nace bazanyi aure ba, harsai nad'auki fansa akan wad'anda suka kashemin iyaye,_

Sai gashi cikin ikon Allah ansamu wata k'ankanuwar yarinya takashe Wasu azzalumai 2 acikin k'auyen gurma wad'anda suna d'aya dga cikin wad'anda nake burin d'aukar fansa akansu dga k'arshe matar tace Sunana *SHU'UMA* wanna Shine kad'an dga cikin lbr na,

Guntu hawaye suka zubowa Ramlat tayi ajiyar zuciya tace "Aunty idan nace miki nice wadda nakashe wad'annan mutanen 2 zakiyarda kuwa?
     Matar tad'an batse fuska tace "bangane ba, ramlat me kike nufu?

Ramlat tace "aunty shu'uma ina nufin nice wadda nakashe mutanen da kike magana acikin k'auyen gurma, wani irin kallo mai d'auke da mamaki shu'uma tayi mata tace

"Ramlat waike wacece kuma mei yasa kika kashesu, menene Labarin ki? duk a lokaci guda tajero mata wad'annan tambayoyi..!! Ramlat tasake da hawaye tace

```"Aunty nima wad'annan mutane sune suka kashe iyayena akan mahaifina yak'i basu goyon bayan su cinye wani filin marayu dake cikin k'auyen gurma wanda hakan ne yasa sukayi meeting dga k'arshe suka yanke shawarar kawarda shi, bazan tab'a manta wann ranar ba ranarda suka k'ona iyayena Acikin mota ranarda zamuje wurinda najima ina mararin zuwa arayuwata da hakan nasha alwashin duk lokacinda nagirma saina d'auki fansa akan cutarda iyayena da sukayi....wannan shine kad'an dga lbr na,```

_Ajiyar zuciya shu'uma tayi tace "Lallai ramlat yazama dole agareni natayaki d'aukar fansa domin mahaifinki yarasa rayuwar sane akan k'wato mana hakk'in mu da yajeyi wannan filin dakike magana tabbas filinmu nea da mahaifin mu yabari wanda a yanxu shine aka gina babbar makarantar da kecikin k'auyen gurma,_

Tashi ramlat tayi taje tazauna akan k'afafun shu'uma tana kuka "kiyi hakuri ramlat tashi kije kiyi wanka kisamu kiyi bacci idan kinfarka kizo muzauna muyi shawara akan hanyarda zamu b'ullowa wad'annan Azzalumai ramlat tad'ago tace kmar suwa kenan Aunty? Shu'uma tace   *"SARKI MURTU da HONORABLE*

Bamusu suka tashi su duka bayan sungama shek'a wankansu suka canxa kaya Alwala sukayi sukayi sallar Azahar sannan suka kwanta dga lokacin ramlat tagane cewa shu'uma musulma ce kwance suke suna firarsu ta duniya dga nan sai barci

 ```Misalin k'arfe 4:00pm suka tashi sukayi sallah shu'uma tajayo ramlat tana nuna mata wasu wurare acikin gdn domin gidane babba mai manya itatuwa da wurin hutu iri-iri anan suka samu wata inuwa mai sanyi suka zauna suka shirya planing ta hanyarda zasubi domin cinma burinsu, ramlat ta k'ara samun kwanciyar hankali sosai fiye da zamanta gidan su Ashraf hakan yasa tasake jiki sosai da Aunty shu'uma da sukaga magriba ta gabato suka tashi suka koma cikin gida sukayi shirin Alwala,```

_Bayan sungama sallar magriba da isha'i dga nan suka fara shirin barci idan kaga SHU'UMA da RAMLAT saika rantse uwa da d'iyace..))_

_((Follow Me With My Facebook))_
https://mobile.facebook.com/Raheem-jega-Novels/976058029184366?ref=opera_speed_dial_freefb

       *MY WAtsapp Group*
     Raheem jega Novels📚
       +2347069242722

Via OHW📲

📚🍀🍒🍀
               *RAMLAT*
           _Yar Tsintuwa_
                           🍀🍒🍀

*_Written BY S.raheem jEga📚_*

             _🍒RaMlaT🍒_
                     *51_56*

*Washe Gari*
_Yau ranace kamar kullum Labarin mutuwar manyan yaran SARKI MURTU yasamu Honarable, tafiyace ya shirya ta mussamn shikad'ai saikuma direban sa, da excort d'insa guda zuwa gaisuwa a k'auyen gurma babbar motarsa ajiye take a harabar gidansa dirabansa shikad'ai yake jira suwuce,_

```Acan gidan Aunty shu'uma tunda sassafe suka tashi itada ramlat dama tunjiya sungama tsara komai ramlat tana sanye da farar rigar mai ratsin bak'i sai kuma sket baki na yara shu'uma tunda dga k'asa har sama komai nata bak'ine tayi shiga cikin bak'aken kaya banda edon ta ba abinda zaka iya ganewa ajikinta,```

```Sukazo dai-dai hanyar da honarable zaibiyo suka buya akan bayan wata bishiya tundaga nesa suka hango motarsa wata kaza naga shu'uma t d'auko ta yankata ta zubarda jinin kazar ajikin ramlat gaba d'aya rigar ramlat ta lalace da jini da sauri ramlat taje ta kwanta akan titi tayi lahu tamkar gawa....^^```

*Direban na k'arasowa honarable yace "dakata usman kataka birki nace..!!*

Yaja birki jikake "keyyyyyy suka fito honarable yad'ora hannunsa ajikinta yaji ko numfashi batayi ya duba ko ina babu alamar mutum d'aukota yayi cike da tausayi yace "usman kajuya motar muje hospital da sauri direba yayi riverse suka koma har Alokacin rungema yake da ita jiyake tamkar yarsa ce ajima kad'an yakai dubansa gareta,

```Shu'uma dake b'oye tana ganin hakan da sauri tafito akayi sa'a mai napep yabiyo tatsaida shi tayi masa kwatancen inda zaikaita basufi minti 5 ba yakaita a k'ofar gidan honarable tabashi kud'insa yatafiyar sa, tsaye tayi tana k'arema gidan kallo har alokacin fuskarta rufe take a hankali tanufi k'ofar shiga gidan tana kai gate taci karo da matar honarable zatafito da mota da sauri takoma baya gabanta na duka tajuya tamaida hankalinta akan titi kmar batasan da gidan ba,```

Saida tadaina ganin motarta sannan tajuyo takutsa kai acikin gidan tanatafiya sum-sum kamr mai gsky tana kai bakin k'ofar shiga palour taji ance "dakata malama wacece ke?

tsaye tayi cakk wuri guda itabata tafiba, kuma batace k'alaba, tsawa yadaka mata "ke malama magana nake  abokinsa ne yadafa kafad'arsa yace

_"Aa Labbo wlh na rabaka ka mnta Alhj yace xayyi bak'uwa yau,  hannu yad'ra abaki yace "nashiga uku ba shakka wannan kayan Alh ce_

Murmushi ya k'irkiro yace "hajiya dn Allah kiyi hkr wlh banxata keceba, dama Alh yasanarda mu zuwanki, kai kawai ta girgixa musu takama hanya sai cikin palour,

Labbo yace "nagode Allah yau dana rasa aikina dariya abokinsa yayi yace "Haba labbo aikai daganin irin wann shiga nata komai arufe basai anfad'ama ba kasan tsarabar Alhj ce, labbo yayi ajiyar zuciya yace "Allah yasa mudace.

Tsaye take a palour tana rabon edo idan tashiga wannan d'akin tafito tafad'a wancan kasan cewar gidan ba kowa da haka harta fad'a dak'in honarable tundaga bakin k'ofa sanyin A.C yafara d'ibarta da tsoro tsoro takai edonta akan wasu file-file dake ajiye akan wata Babbr Akwatinsa koda taduba duk file nea na gidaje da filaye harda na kamfanonin sa,

_Nan tashiga bincike duk saida tagama dubesu kaff bataga takardun filin mahaifinta ba, hannu tasa tabud'e Akwatin File tagani d'auke da sunan mahaifinta hakan ya tabbatar mata da cewa tabbas wad'annan sune takardun filayen mahaifinta d'aukowa tayi tabaro d'akin da sauri tamayarda nik'ab d'inta batare da kowa yaga fitarta ba, tatari mai Napep yace "hajiya ina zamuje tace "Sabon gari....))_

          *HOSPITAL*
```Darect Asibitinsa, sukaje yashigo rungume da ita hannunsa da gudu Likitoce sukayo kansa ganin cewa honarable ne da kansa yazo da marar Lafiya hospital emergency room Akakaita yasanar da likita cewa sukala da ita Ayi mata duk abinda yakamata, xaije wani k'auye nanda hour 3 zaidawo har Alokacin honarable baigane fuskar ramlat ba,```

*Likita yayi bincike baiga ko k'warzane ajikin ramlat ba, toh kuma mei yabata mata jiki da jini haka itace tambayr  da yakewa kansa, ajiyar zuciya yayi yace "Allah yasawwak'a yafita yakoma office d'insa,*

_Bayan shu'uma takai takardun gida ta'ajiya wanka tayi ta canxa kaya tasa atamfa tayi make up tad'auki mayafinta tafito murmushi tayi tace "Allah sarki ramlat yarinya mai hankali ga natsuwa kuma ga wayo Amma anhana iyayenta su ribanci rayuwarta, tayi ajiyar zuciya tace "toh yanxu A wace hospital yakaimin ramlat? Duk azuci take wann zance kawai ta yanke shawarar bari tafara zuwa hospital d'insa,_

Via OHW📲📚

🍀🍒🍀
               *RAMLAT*
           _Yar Tsintuwa_
                           🍀🍒🍀

*_Written BY S.raheem jEga📚_*

             _🍒RaMlaT🍒_
                     *56_60*

```IHSAN HOSPITAL```
Aka ajeta da shigarta darect side d'in yara taje, saidai batasan a wane d'aki akakai ramlat ba, wani doctor ne yasameta a tsaye yace

_"Malama wakike nema? tace "yawwa d'azu da safe wani babbn mutum yazo da wata yarinya anan wadda tayi tana sanye da fararen kaya, doc yace "ko honarable kike mgn tace "ehh shine, yanuna mata d'akin tayi masa godiya tawuce,_

*Da shigarta d'akin ramlat naganinta wani farin ciki yaziyarci zuciyar tatashi zaune tace*

"Aunty shu'uma waya gayamiki inanan zare edo tayi tace "Aa ramlat kwanta pls karki manta wannan fa duk shirine mukeyi, komawa tayi kwance da sauri shu'uma tace "ina Azzalumin yake?

Ramlat tace "yatafi gurma amma anjima kad'an zaidawo Aunty ina fatar kingano inda takardun suke tayi murmushi tace "eh ramlat yanxu naki shirin kawai yarage dan haka karkiyi wasa,

_ta girgixa kai tace tohm aunty kitashi kitafi karyaxo yasameki anan, shu'uma tace "shikenan ramlat nizantafi,_

```Tana d'ora hannunta da nufin bud'e gambun d'akin taji anjaye gambun karaff tafad'a ajikinsa, saida purse d"inta yafad'i da sauri ya d'auko mata yace "i'm sorry kai ta girgixa tace "bkm tawuce shikuma yashigo d'akinda ramlat take, murmushi yayi ganin ta dayayi afarke yace "yace sannu yarinya murmushi kawai tayi masa jiyayi tak'ara shiga rainai,```

Doctor yace "ranka yadad'e zaku iya tafiya da ita a yanxu munbin cika babu wani rauni ajikinta kawai buguwane tayi Amma tana buk'atar hutu sosai,

honarable yace "Ohk mungode sosai direban sa yad'auki ramlat sukafito yasata a mota basu wuce gidaba saida suka biya super market a kayimata shorpping sannan suka dawo gida koda yaxo ya taradda hajiya batanan sunjima a palour tare da d'iyarsa guda wacce shekarunta basufi 10 ba ana kiranta da IHSAN,

      *_BAYAN KWANA BIYU_*

Ihsan da ramlat sunfara shak'uwa da jununsu hajiya matar honarable tana nunawa ramlat so da k'auna kusan ince komai za'ayiwa ihsan tare a keyimusu itada ramlat,
    Yau dai ranace kamar kullum ramlat tatashi ranta ab'ace ita adole sai ankaita gida Wasa wasa harta fara kuka ganin haka hajiya ta lallasheta tace tabari idan kawunta yadawo zaikaita,

 ```honarable na dawowa Akasanr dashi cewa ramlat ta'aza kuka ita gida zataje, yasa aka kirata yace "ramlat gida zakije tace "ehh dariya yayi yace toh inane gidan naku tanuna masa k'ofar fita da yatsa duka suka d'auki dariya ganin tabata rai yace "Aa ramlat dole inkaiki gida jeki kira Ihsan tarakamu,```

_Da gudu tanufi d'akinsu ihsan na bacci ta tayarda ita tace tazo taraka gida ihsan sai farin ciki takeyi dama tanason tasan mamar ramlat suka rik'o hannun juna suka fito duk azaton honarable ramlat wasa  takeyi zasufita ne ramlat ta kalli haj. tace hajiya sai wata rana murmushi tayi tace_

 *"tohm ramlat adawo Lfy hajiya da honarable sufa duk a wasa suka d'auki abun suka fito yabud'e musu mota suka shiga da kansa yaja motar aka bud'e masa gate yafito yace*

to ramlat yanxu ina zamubi tanuna masa hanya duk kwanarda akaje saita nuna masa da haka harsu kakai sabon gari dai-dai k'ofar gidan Shu'uma sukayi parking tafito tarik'a hannun ihsan shidai hornbl mamaki duk yacikashi suna gaba yana biye dasu harcikin gida,

_Zaune take a palour kwatsam taga ramlat tare da honarable harda 'yarsa Azuci shu'uma tace "uhmm Lallai ramlat sai yau nak'ara shaida cewa ke 'yar halak cea,......))_

🍀🍒🍀
               *RAMLAT*
           _Yar Tsintuwa_
                           🍀🍒🍀

*_Written BY raheem jEga📚_*

             _🍒RaMlaT🍒_
                     *61_66*

_Fuska cike da fara'a shu'uma tatarbi su honarable, ruwa taje tad'auko tazuba mai a cup shida d'iyar IHSAN yakarb'a yana yake azuciyarta jitake kmar tasa hannu tashak'e masa wuya sai  ya d'auke wuta,_

Bayan sungama gaisuwa shu'uma tayi musu godiya dga k'arshe harda hawayen k'arya ta k'irk'ira tace
     "Bansan da wace irin kalma zanmaka godiya ba, yau kusan kwana 3 kenan rabona da ramlat dga zuwa makarnta bank'ara sata a edo naba,

"Allah sarki ba kuka zakiyiba kamata yayima Allah gdy da yasa 'yarki bata fad'a nugun hannu ba, bayan tagama yimai godiya ihsan na zaune ajikin shu'uma duk a zatonsu mamar Ramlat ce wani kallo honarable kema shu'uma "anya kuwa banwayi wanan fuskarba, ya fad'a azuci ganin irin kallon da yake mata yasa ta sauke IHSAN tatashi tace
   "Ina zuwa ranka yadad'e yace "tohm" darect d'aki tanufa tabar honarable zaune a palour shida Ramlat da Ihsan,

```Da shigarta ta mayarda gambu tarufe tashiga canxa kaya dogon wando tasaka tare da rigar k'ananan kaya kmar tasanyi kana ta sanya wata bak'ar hula ko ina nata akame ba shakka daganin wannan dressing nata Nasan shirin d'aukar fansa nea akayi, wata sharb,ebiyar wuk'a🗡 tad'auko tab'oyeta acikin jikinta, Ajiyar zuciya tayi sannan tafito suna had'a edo da Ramlat tad'agama ramlat gira nan naga ramlat tatashi taje tarufe gambun paloun jikake gumm, da sauri ya d'ago kai yace "Ramlat Lfy kuwa?```

Shu'uma tace "Lafiyar kenan ai" sai a lokacin ya luracewa shu'uma na tsaye akansa, mamaki ya bayyana a fuskarsa k'arara kafin yay magana, shu'uma tace

"Ramlat kenan Nasan baxaka tab'a manta da *Alhj Hisham* ba, wanda karabashi da duniya akan kwad'ayin dukiya, dubeta kagani ramlat cea d'iyar gidan mak'iyinka Alhj Hisham k'aramar yarinyace Amma bazata tab'a mantawa dakai arayuwarta ba,

tabuga hannunta a k'irji tace cike da hargowa tacw "Nice *SHU'UMA* 'Yar gidan Alhj mukhtar  kakashemin mahaifina akan kawai yahanaka mallakar filinda ba hakk'in ba, kuma kakashemin yayana wanda shuk'uwa ta dashi tawuce misali,

_Duk jikinsa ya mutu zuciyarsa rad'au zafi kalaman shu'uma sunk'ona mai zuciya Afusace yayo kanta yahauta da kokawa dama Ashirye take sukayi arangama yajefata akan mirrow ya sake shak'o wuyanta ganin haka Ramlat tayo kan Ihsan da sauri tad'ora mata wuk'a awuya.....!!_

```Madadin yaga tayi yunk'urin k'wace kanta sai gani yayi tana dariya tana nuna IHSAN da yatsa koda yajuya edonsa yagane masa ramlat dake k'okarin kashemai d'iya da sauri yasake shu'uma yajuya danufin ceton 'yarsa Sharff yaji shigar wuk'a Acikinsa, kanyayi wani motsi tak'ara sokamai ita harsau 3,```

*Ya sulale ak'asa yana mai kallon 'yarsa IHSAN jini yayi inda yakeso da gudu tataso tana kiran BABA......))*

Murmushi ramlat tayi datatuno lokacinda take kiran mahaifinta yayinda wuta take k'unarsa yau gashi honarable naji 'yarsa nakiransa Amma zaitafi yabarta,

Acan gidan honarable hankalin hajiya bai kwanta ba, tunda safe honarable yabar gida gashi har ankiran sallar Azahar baidawo ba, wasa wasa har 3:pm babu lbrn honarable nanfa rigama rakaure hajiya duk ta haukace ankira wayoyinsa kowace Akashe tofaaaa...^^

*Bari mulek'o bangaren su Aunty shu'uma da Ramlat*

cikin gaugawa suka kwashi gawarsa suka saka a butt d'in motarsa suka d'aurewa ihsan baki suka sata a mota shu'uma taja motar sai k'ofar gidan honarable tayi parking saida suka jira mutanen da ke wucewa sungama wucewa sannan suka fito sukabar motar nan suka tari napep suka koma batare da kowa ya gansu ba,

 Dawowar Labbo mai gadi dga masallaci Tun daga nesa ya hango motar honarable ak'ofar gida bud'e bakinsa yace "nashiga ukuna yau narasa aikina tunda honarable yadawo bai taraddani a k'ofar gida ba,

Yak'arasa gurin motar yarega baiga kowa acikiba, ihsan kuwa tanaso tayimai mgn bakinta arufe, da gudu yanufi cikin gida,  Zaune take fuska a d'aure rashin dawowar Alhj gida shine babbn abinda ke damunta kwatsam yashigo palour kamar wanda aka koro a tsorace haj. tad'ago kai tace "Lfy Labbo waya biyoka?

```Yana huka yace "Bakomai hajiya wurin Alhj nazo nabashi hakuri,  tundazu yazo yana jirana banxo na bud'e gate ba haryayi fushi yabar motar a k'ofar gida, dajin haka batajira yak'arasa maganr ba tafigi mayafi tureshi tayi yafad'a cikin flowers da ke tsakiyar palour tanufi inda motar take, Ma aikatan gidan suka mara mata baya da zuwanta bata jira komaiba tabud'e murfin motar saiga IHSAN tafad'o ak'asa kamr wadda akajefo zare edo tayi takira sunannta cikin gigita IHSAN hannu tasa ta kwance mata baki, ihsan tayi ajiyar zuciya tafashe da kuka ta rungume hajiya,```
      _Hajiya "tace ina Abban ki? Nuna butt d'in motar tayi tana kuka koda akaje usman direba yabud'e butt saiga honarable kwance cikin jini babu alamar numfashi tare dashi Nan hajiya ta sulale Ak'asa somammiya Nan take lbr yagame gari Aka kwashi gawar honarable shida matarsa darect IHSAN HOSPITAL aka nufa,_

*Al'amari ya cab'e bari mulek'o muku k'auyen gurma muji halinda Ashraf da k'anwarsa suke ciki Yanxu😜*

    *```MY Facebook Page```*
 https://mobile.facebook.com/Raheem-jega-Novels/976058029184366?ref=opera_speed_dial_freefb

      *_MY Watsapp Group*_
       Raheem jEga Novels📚
        +2357069242722

Via OHW📲📚

🍀🍒🍀
               *RAMLAT*
           _Yar Tsintuwa_
                           🍀🍒🍀

*_Written BY raheem jEga📚_*

             _🍒RaMlaT🍒_
                     *71_76*

_Ramlat naganin sunyo kanta juyawa tayi tashiga jeji gata da shegen gudu haka suka biyota suna ihu suna jifanta da mashi k'arar bindiga kawai kakejin yana tashi amma hakan baitayar mata da hankaliba, kasan cewar yarinyace marar tsoro biye suke da ita babu sassauci sai ratsa ciyawa take tana k'arawa,_

```Acan k'ofar gari sauran dakarun sarki suka bud'e k'ofar domin suje sushaida ma Shugaba cewa Ankama Ramlat tananne Shu'uma tasamu takutsa tashiga garin batatsaya ko inaba, sai darect sai gidan su Ashraf, tararda umma cikin damuwa duk ta rame Akullum cikin kuka take da kuma tunanin 'Yayanta 2 da'aka kama ana azabtar dasu, a gidan SARKI,  shu'uma ta sallama umma ta amsa murya a mak'ure domin a kullum cikin kuka take harya muryarta ta canxa, hankalin shu'uma yatashi sosai jikinta yayi sanyi Azuce tace "Nashiga uku inda bakashe``` *ASHRAF da HUMRAT* ```Akayiba.
     Bayan sungama gaisawa shu'uma take tambayar ta "me yasakata cikin hali nadamuwa "meke faruwane umma? Nan umma takwashe labari komai tafad'a mata, ajiyar zuciya shu'uma tayi kafin tace```

"Kidaina kuka umma kid'auka dga yau wannan damuwar takau kuma Ramlat Nanan araye daga yanxu zuwa wayewar safiya Namiki alqawarin fitowa da Ashraf shida k'anwarsa a gidan Azzalumin sarki, cike da farin umma ta rungume sh'uma tace "duk da cewa bansa waye keba, dole inmiki godiya kuma namiki alqawarin idan har kika tabbatar da maganr da kikafad'a zanbaki duk abinda kekada buk'ata Na rayuwa,

*"Dariya tayi had'e da murmushi tace "kikwantar da hankalinki umma da sannu zakisan ko waceceni,*

Acan cikin jejin gurma jeji mai hatsari jejinda ke d'auke da mugayen ababa, Acikinsa nea Ramlat taja mutanen Sarki murtu domin kawai tad'auki hankalin su shu'uma tasamu shiga cikin garin gajiya tafara kama ramlat gashi harbinta ake da kifiyoyi🏹 tana kaucewa tanemi inda zata b'uya tarasa juyowa tayi ta kalli dakarun da kebiye da ita, hawaye ne suka zoba a edonta tafashe da kuka domin ganin taron da batasaba ganin irinsa ba kuma duk ita suke biya,

Kuka take tana gudu tana kiran Aunty shu'uma dabara tab'ace mata cantayi tuntub'e da wani icce tafad'a Acikin kwalambon ruwa jikinta duk yab'ace ananne suka samu damar kamata da isowarsu babban daga cikinsu ya wanketa da wani irin lafiyayyen mari a fuska saida jini yafito a bakinta taratsa wani irin kuka yasake shurinta Aciki yatsamota dga cikin ruwan yad'orata Akafad'ar sa suka biyo hanya suka dawo sai fadar gidan SARKI suka sauketa,
            Jama'ar gari kokuwar shiga sukeyi a gidan sarki domin suga wacece wannan Ramlat, fadawa suka hana kowa shiga Sarki kuwa cike da gadara yasauko dga kujerarsa yaxo gaff agabanta ya tsaya and'orata Akan kujera d'ago kanta yayi ya k'ureta da edo jiyake kamar yasa takobi yacire mata kai, sai kuma ya girgixa kai domin ganin yayi tayi k'ank'anuwa, Azuce yace "sam baidace ace kalar wann yarinyar ce take aikata wannan mummunan kisaba,

```Matarsa kuwa dataji labarin cewa Ankama Ramlat Afusace tazo da isuwarta tad'aga hannu zata mari Ramlat Sarki ya dga mata hannu ya girgixa kai yace```
   ```"Wann bashine huce haushi ba, bana buk'atar kowa yasake dukanta inason ayi sanarwa agari cewa gobe k'arfe goma na safe ana buk'atar kowa a mujami'a domin ganin yanda za'a yankewa Ramlat hukunci itada mai lek'en Asirinta watau Humrata, dga k'arshe yace atafi da ita wurin jakadiya Ayi mata wanka acanxa mata kaya kuma kuma abata tsaro mai tsanani,```

_Ashraf yasamu labarin cewa Ankama ramlat kuma gobe za'ayimata hukunci agaban jama'a yasan ba shakka Sarki kashe Ramlat zayyi domin yasanar da hukumar 'yan sanda YOBE cewa ankama wacce takashe honarable,))_

        *```MY FACEBOOK PAGE```*
 https://mobile.facebook.com/Raheem-jega-Novels/976058029184366?ref=opera_speed_dial_freefb

           *MY Watsapp Group*
        _Raheem jEga Novels_
          +234769242722

Via OHW📲📚

?🍒🍀
               *RAMLAT*
           _Yar Tsintuwa_
                           🍀🍒🍀

*_Written BY raheem jEga📚_*

             _🍒RaMlaT🍒_
         *76_80*

_Ramlat naganin sunyo kanta juyawa tayi tashiga jeji gata da shegen gudu haka suka biyota suna ihu suna jifanta da mashi k'arar bindiga kawai kakejin yana tashi amma hakan baitayar mata da hankaliba, kasan cewar yarinyace marar tsoro biye suke da ita babu sassauci sai ratsa ciyawa take tana k'arawa,_

```Acan k'ofar gari sauran dakarun sarki suka bud'e k'ofar domin suje sushaida ma Shugaba cewa Ankama Ramlat tananne Shu'uma tasamu takutsa tashiga garin batatsaya ko inaba, sai darect sai gidan su Ashraf, tararda umma cikin damuwa duk ta rame Akullum cikin kuka take da kuma tunanin 'Yayanta 2 da'aka kama ana azabtar dasu, a gidan SARKI,  shu'uma ta sallama umma ta amsa murya a mak'ure domin a kullum cikin kuka take harya muryarta ta canxa, hankalin shu'uma yatashi sosai jikinta yayi sanyi Azuce tace "Nashiga uku inda bakashe``` *ASHRAF da HUMRAT* ```Akayiba.
     Bayan sungama gaisawa shu'uma take tambayar ta "me yasakata cikin hali nadamuwa "meke faruwane umma? Nan umma takwashe labari komai tafad'a mata, ajiyar zuciya shu'uma tayi kafin tace```

"Kidaina kuka umma kid'auka dga yau wannan damuwar takau kuma Ramlat Nanan araye daga yanxu zuwa wayewar safiya Namiki alqawarin fitowa da Ashraf shida k'anwarsa a gidan Azzalumin sarki, cike da farin umma ta rungume sh'uma tace "duk da cewa bansa waye keba, dole inmiki godiya kuma namiki alqawarin idan har kika tabbatar da maganr da kikafad'a zanbaki duk abinda kekada buk'ata Na rayuwa,

*"Dariya tayi had'e da murmushi tace "kikwantar da hankalinki umma da sannu zakisan ko waceceni,*

Acan cikin jejin gurma jeji mai hatsari jejinda ke d'auke da mugayen ababa, Acikinsa nea Ramlat taja mutanen Sarki murtu domin kawai tad'auki hankalin su shu'uma tasamu shiga cikin garin gajiya tafara kama ramlat gashi harbinta ake da kifiyoyi🏹 tana kaucewa tanemi inda zata b'uya tarasa juyowa tayi ta kalli dakarun da kebiye da ita, hawaye ne suka zoba a edonta tafashe da kuka domin ganin taron da batasaba ganin irinsa ba kuma duk ita suke biya,

Kuka take tana gudu tana kiran Aunty shu'uma dabara tab'ace mata cantayi tuntub'e da wani icce tafad'a Acikin kwalambon ruwa jikinta duk yab'ace ananne suka samu damar kamata da isowarsu babban daga cikinsu ya wanketa da wani irin lafiyayyen mari a fuska saida jini yafito a bakinta taratsa wani irin kuka yasake shurinta Aciki yatsamota dga cikin ruwan yad'orata Akafad'ar sa suka biyo hanya suka dawo sai fadar gidan SARKI suka sauketa,
            Jama'ar gari kokuwar shiga sukeyi a gidan sarki domin suga wacece wannan Ramlat, fadawa suka hana kowa shiga Sarki kuwa cike da gadara yasauko dga kujerarsa yaxo gaff agabanta ya tsaya and'orata Akan kujera d'ago kanta yayi ya k'ureta da edo jiyake kamar yasa takobi yacire mata kai, sai kuma ya girgixa kai domin ganin yayi tayi k'ank'anuwa, Azuce yace "sam baidace ace kalar wann yarinyar ce take aikata wannan mummunan kisaba,

```Matarsa kuwa dataji labarin cewa Ankama Ramlat Afusace tazo da isuwarta tad'aga hannu zata mari Ramlat Sarki ya dga mata hannu ya girgixa kai yace```
   ```"Wann bashine huce haushi ba, bana buk'atar kowa yasake dukanta inason ayi sanarwa agari cewa gobe k'arfe goma na safe ana buk'atar kowa a mujami'a domin ganin yanda za'a yankewa Ramlat hukunci itada mai lek'en Asirinta watau Humrata, dga k'arshe yace atafi da ita wurin jakadiya Ayi mata wanka acanxa mata kaya kuma kuma abata tsaro mai tsanani,```

_Ashraf yasamu labarin cewa Ankama ramlat kuma gobe za'ayimata hukunci agaban jama'a yasan ba shakka Sarki kashe Ramlat zayyi domin yasanar da hukumar 'yan sanda YOBE cewa ankama wacce takashe honarable,))_

        *```MY FACEBOOK PAGE```*
 https://mobile.facebook.com/Raheem-jega-Novels/976058029184366?ref=opera_speed_dial_freefb

           *MY Watsapp Group*
        _Raheem jEga Novels_
          +234769242722

Via OHW📲📚

🍀🍒🍀
               *RAMLAT*
           _Yar Tsintuwa_
                           🍀🍒🍀

*_Written BY raheem jEga📚_*

             _🍒RaMlaT🍒_
                     *81_85*

_Yau Ranace kamar kullum angayyato Al'umma kamar yada sarki yabada umurni hatta da shuwaga bannin wasu k'auyukan dake kusa da gurma duk sun halarci gidan SARKI MURTU domin ganin hukuncin da sarki zayyanke Akan wann yarinya dake kissanda Ko babban mutum bazai iyashiba,_

Fadar sarki tacika Al'ummar gari kuwa suna dga waje sunyi Asembly kowa jiran yake afito da Ramlat dan suga wane irin hukunci ne za'a yanke mata,    Zaune take akan kujera tsakiyar fadar sarki kowa yayi tsit Ana sauraren bayaninsa, shu'uma tsaye take Acikin taron hannunta d'auke da wani Abu acikin farin k'yalle tak'ure sarki da edo tana sauraren jawabin da yakeyi, a b'angaren umma kuwa k'aramin kasko nea a  hannunta Acikinsa kuwa barkono ne zallah, Asirce take A,azawa Acikin fadar batare da kowa ya lurada abinda takeba, kasancewar kowa yamaida hankalinsa, a wurin SARKI. K'arasowar sojojin YOBE a wurinne Sarki yamik'e tsaya da nufin fita waje agabatar da Ramlat a edon kowa kafin a yanke mata hukunci d'aure take da igiya anrufe mata edo da bak'in abu batasan a ina takeba a lokacin  Shu'uma na ganin haka,

```Tafito da abinda ke hannunta ganinayi ta bud'e k'yallen ta wurgashi Atsakiyar taro mei zangani Ashe dakakken yajine aciki Nantake wuri yaturmuk'e da yaji wasu ko cikin edonsu yafad'a a b'angaren umma tana ganin haka tashiga kunna Wuta tana sakama kaskayen da tajera buraren yaji yatashi hayak'i yaturnuke fadar wuri ya yamutse mutane suka fara guduwa Ramlat na ganin haka ba shakka tasan Aikin shu'uma ne zame jiki tayi tasulale Ak'asa takama rarrahe tanabin k'afafun mutane harta b'ace Acikin taron shu'uma k'okarin ratsa mutane take tana son takai inda SARKI tana kai gaff dashi sukayi edo hud'u kafin ya aikata wani abu tuni tawatsa mai yaji a edo tasa hannu tatoshe mai baki tajashi zuwa wani gurin na daban sukaci gaba da fafatawa,```
       _Bangaren umma kuwa Darect wurin su Ashraf tanufa tataradda dakarun sarki duk sunb'are sunnufi fada kasan cewar abinda ke faruwa a wannan lokacin kowa takansa yake umma tafito da Ashraf suka nemi humrat sama da k'asa basu sameta ba,_ 

Acan cikin fadar ganin abin yacitira sojoji suka fara dukan mutane suna harba bindiga sama Nan take gari yarikice mutanen da ke waje suka fara guduwa ganib haka umma tafasa kuka Ashraf yajawo hannunta yace "umma kizo mugudu, dan Allah tadaka mai tsawa tace

*"Ashraf bazan tafiba idan harbanga humrat ba, yace "Aa umma kixo mutafi nace Nasan akanmu kad'ai Ramlat tamik'a kanta a hannun Sarki bawai kamata akayiba, kuma bazata bar wann gidaba harsai tare da humrat dan Allah kizo mutafi yaja hannunta tana kuka tana kiran yarta humrat.....))*

```Suna fita dga gidan kamar inda Akatashi borm haka sukaga gidan sarki yakama da wuta, babbab tashin hankali fadawa sukanemi sarki babushi ba Alamarshi Ananfa Suka shiga sarar mutane wasu kuma suna harbin mutane da bindiga,  koda su Ashraf suka eso gida suka taradda humrat kwance kamar gawa ramlat tad'ora kanta ajikinta tana kuka firgata hanama ummayin mamakin fitowae ramlat da humrat a gidan sarki afirgice umma taya kanta da sauri tace "wayyo Allah sunka shemin 'Yata umma tashiga jijjigarta tana kiran 'yata dan Allah kada kimutu dafa kafad'arta dataji yayi shiya yad'ago da ita ta kalleshi bud'e bakinsa yace```

_"Ramlat mei yasamu humrat ta mutune? girgixa kai tayi kafin tace "wanine ya harbeta da bullet yayinda naje kwance ta agidan sarki,_

Ashraf yaciro umma ajikinta yana lallashinta yace "umma bata mutuba harbine kuma zatatashi da yardar Abin bauta, a yanxu bamuga ta zamaba, dole mufita mubar garinnan nasan yanxu bada jimawa ba, dakarun sarki nanan zowa agaremu, harararda da umma tayi masa yasa yasoke kai k'asa tace "Lallai hakane wato mutafi mubarta anan tunda muna son mutsirarda rayuwar ba, girgixa kai yayi yace "yace bahaka nake nufiba umma ni zangoya ta abayana mugudu mubar wann garin bayan sunshirya Ashraf ya goya humrat a bayansa, suna fitowa sukaci karo da Shu'uma ta goyo wani abayanta tarufeshi da wani Bak'in mayafi da gudu ramlat taje ta rungumeta tace

"Aunty ina fatar kingama da waccan Azzalumin? Murmushi tayi kafin tace "Alqawari ne nad'auka ba wanda zaikashe sarki face kee dan haka yasa nasace shi nad'aureshi nagoyoshi abaya domin inxomiki dashi kid'auki FANSA.......!!

     *MY Facebook Page*
https://mobile.facebook.com/Raheem-jega-Novels/976058029184366?ref=opera_speed_dial_freefb

Via OHW📲📚

🍀🍒🍀
               *RAMLAT*
           _Yar Tsintuwa_
                           🍀🍒🍀

*_Written BY raheem jEga📚_*

             _🍒RaMlaT🍒_
                     *86_90*

          *LAST PAGE*

```Zare edo Ashraf yayi ya kalli shu'uma ya kuma kalli Ramlat yace "'yar tsintuwa ita kuma wannan waye? Murmushi tayi tace "Ya Ashraf wannan itace sh'uma haka take tamkar uwa agareni itama haifaffiyar wann garince tarasa iyayen tane da kuma 'yan uwanta kamar yanda narasawa, itace tataimaka min harna cinma burina, "Ya Ashraf kabata hannu kuyi musabuha```

Yabata hannu itama tabashi suka gaida juna, d'ago kai da umma tayi tace "kunga kozo mugudu mubar garinnan ba shakka a duk inda dakarun sarki da sojoji suke musuke nema,  wata hanya suka kama Acikin jeji tafe suke Amma duk hankalinsu Atashe fad'i tashi sunyi nisa Acikin jejin abayan su kuwa biye ake dasu ana neman su, kota halin k'aka

```Gari duk yaya mutse Anrasa rayuka da dama wasu kuma anmusu rauni, cikin ikon Allah har sukayi nisa da garin ba'asamu kamasu ba, har Alokacin humrat bata farka ba,Anan sh'uma tasauke Sarki dake goyo abayan ta an d'addaure shi da igiya fuskarshi jina-jina bak'aramin duka yashaba a wurinta yayinda suka fafata shida ita acikin gidan sa har Allah yasataci k'arfinsa da dabaru.  ,bata lura da rauninda yayi mataba saida suka tsaya Suka samu wani rafi sukasha ruwa bayan sunhuta Ramlat tazo agaban sarki ta tsaya, tasa kafarta takai masa duka harsaida ya farfad'o dga suman da yayi a hankali yabud'e edo ya kalleta yak'ara kai duban sa ga Ashraf nan yagane ko suwaye, ya yunk'ara yatashi amma ba dama sbd yasha d'auri bud'e bakin Ramlat tace```

"SARKI MUTU Yau ramlat cea 'Yar gidan Alhj hisham, kun kashemin iyayena a lokacinda nikeda buk'atarsu tanuna shu'uma da hannunta tace "wann kuma shu'uma kenan 'yar gidan Amininka Amma Akan kwad'ayin abinda duniya kabada goyon baya Akakashe mata uba kamai da ita marainiya wann kuma shine Ashraf

Wanda ka k'ulla soyayyar sa da 'yarka badan Allah saidan kacinma wata manufa taka SBD ka k'wace sarautar sa da mahaifinsa yabar masa, to yau mune Akan ka, mukazo d'aukar fansa Agareka kuma nida kaina zankashe ka, d'aga wuka tayi sama zata soka masa umma ta d'aga mata hannu "dakata Ramlat,

Kafin kikashe shi inason nak'aramai tabo Azuciya' kamar yadda ka kashemin miji akan kwad'ayin sarauta to yau da hanuna nakashe matar ka, Lubna dama nafad'ama komai dad'ewa zaka k'are a wulakance, kuma gashi kagani da edonka d'aga k'afa tayi takaimai shuri a fuska tace Natsane ka MURTU bud'e bakinsa yace "dan Allah kada kukasheni, wlh natuba kuma nayi dama, jin maganar sa wani haushi yake k'arawa Ramlat kafin yarufe baki, tadaka mai wuk'ar azuciya tasake tasoka mai ita Aciki yayi ihuu duk saida dajin ya amsa K'arar ihunsa shiya tada humrat ta farfad'o da sauri Ashraf ya rufe mata edo dan karta ga abinda ke faruwa tasake somewa,

 Anan suka bar gawarsa Ramlat farin ciki yamamaye zuciyarta yau burinta ya cika tsalke tayi tahaye bayan Shu'uma humrat kuwa Ashraf ya goyata suka nufi wani k'auyen Anan ne suka samu bagiren zama aka tarbesu hannu biyu aka basu masauki, suka zauna cikin kwanciyar hankali,

   ```BAYAN KWANA 2
Humrat tasamu Lfy ba abinda suka rasa, na rayuwa Acikin k"auyen Ramlat kuwa sai k'ara girma takeyi```

Bayan wasu watanni sun had'u suduka a gida suna firarsu cike da zolayar juna,((umma)) tad'auko zancen Aure tace ma Ashraf  yaje yanemi budurwa kyakkyawa mai sonshi Acikin k'auyen yaxo a d'auramai  aure da ita,
     Cikin tsokana Ramlat tace "abu mai sauk'i gamu da kyakkyawar budurwa acikin gida kawai umma kihad'ashi shida Aunty shu'uma tak'arasa mgnr cike da dariya....😜

Ashraf yabita tagudu taje baya umma ta b'uya yace "yau bamai rabani dake bata k'amarki tsokana ba, umma tace "Aa ba abinda zakamata ai Gsky tafad'a barima kaji nan zuwa jibi za'a samuku rana dan haka kutai kusha soyayyar ku...!!

Dariya humrat tayi mai had'e da gwalo ta fixgo mayafin shu'uma tazo ta lauya mai Afuska yabita da gudu haka sukayini sunata tsokanarshi shida shu'uma, wasa-wasa abu harya xama gsky Aka k'ulla aure tsakanin Ashraf da shu'uma zokaga yanda ake soyayya Ramlat kuwa tafi kowa farin ciki tazama kamar err lele kowa k'aunarta yake Yarinya mai Ashraf da Shu'uma Ramlat kenan hakadai rayuwa tacigaba da tafiya..

Acan kuma k'auyen gurma bayan komai yalafa duk wata k'ura tawuce Masarautar ta koma kamar sabuwa a yanxu hka dai HAYBA itace take rik'e da masarautar garin, mulki yasa tamanta komai rayuwarsu suke cikin kwanciyar hankali kamar komai baitab'a faruwaba,

Hausawa sukace Laifin dad'i k'arewa..!! Anan nakewa cewa Bissalam.

      *ALHADULILLAH*
     

 *```GODIYA```*
_ga Allah mad'au kakin Sarki wanda Yanunamin Na kammala wannan k'aramin littafi Nawa bisa baiwar da yayimun batare da Nabiyasa ba,_

        *SADAUKARWA*
```Na saudau karda wanann Littafin nawa ga d'an uwana kuma k'aneNa``` *IKRAMA IBRAHIM ISA JEGA* _Group ADmin AREWA24 Allah Yabarmu tare Ya karemu da sharrin masu sharri_

           *GODIYA* 2
Ina mik'a godiya Agareku members d'in Raheem JEga Novels📚 Allah kara had'a kanmu Yak'aro zumunci mai d'orewa

```Kai kam Yazamo dole agareni Na Ambace ka babban Aminina Abdul-mr smile😃 tare mukazo tare Aka ganmu kuma a haka za'a barmu da ikon Allah "Allah karemu da masu hange. Nesa,```

 ```GAJINJINA TA AGAREKU MASOYAN WANN BOOK NAWA MAI TAKEN SUNA RAMLAT 'YAR TSINTUWA```
        _Na gode fans Kuci gaba da kasan cewa atare dani Naku Raheem jEga📚 kecewa kufuta Lafiya_

Domin samun Littafaina Akai tsaye ta hanyar Facebook zaku iya like d'in page d'ina
 https://mobile.facebook.com/Raheem-jega-Novels/976058029184366?ref=opera_speed_dial_freefb

  Daga k'arshe ina muku bankwana duk wanda nayima ba dai2 ba Namiji/mace dan Allah Yayafemin😭👏🏻   Anan nake cewa..!!

     *SAI WATA RANA*😪
Copied By
HAYATU BABA ZUBAIRU
        (admin
       Novels villa
     Duniyan novels 
   Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
          And
Cool novel, makeup and cooking) 

      WHATSAPP NO:
       07039625239

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *