Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Sunday, December 2, 2018

AISHA HUMAIRA Complete hausa novel

adsense here
AISHA HUMAIRA Complete hausa novel
[6:25PM, 3/14/2017] Kairat Up: [16:01, 09/01/2017] khairat up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨

*1*

   *Aisha humaira*
     *Aisha humaira*
!!wai kina ina ne yar nan ina kiran ki kina jina amma kika min shiru ko se na shigo dakin?
  Zaki fito ko sena shigo!
  Bakin ta kamar ya hade da bango tsabar tsiri dan masifa
   Ke da'ada wai kin fiya takurawa mutum wallahi Allah
  Ta jefe ta da cokalin hannun ta
 Kaucewa ta yi hade da kyal- kyalar dariya ta dau bokiti tayi hanyar bangaren baffa idi tana yan wake-wake.
   Baffa na alwala a tsakar gida ya daka mata tsawa ke wai aisha humaira yaushe zaki nutsu ne ki shigo gida ba sallama se wake.
      Yi hakuri baffa na tuba
Kullum a haka kike ai dama kin tuba.
Sum sum ta shige cikin gidan
Inono na kan sallaya tana lazimi haba ta rike cike da mamaki a ranta tace wannan yarinyar da shakinyanci take
   Inono ina wuni
Kai ta gyada mata saboda lazimi ne a bakin ta.
  Inono ina fatima bintu?
  Daki ta nuna mata bokitin ta ajiye a tsakar falo ta yi cikin dakin da gudu fatima bintu na bacci taji an fado mata a ka
Ihu ta zunduma tsabar tsoro tana mikewa kuwa aisha humaira tasa mata dariya harda tsugunawa kasa
  Fad'ima bintu ta tsuguna ta gartsa masa cizo a kunnen ta tsalle ta daka tana ihu
 Inono ta shigo da sauri da carbi a hannun ta wallahi se kun fita daga gidan nan wallahi yanzun nan na rantse da girman Allah.

   Suka yi waje da gudu.
  Aiko suka ci karo da hamma yusuf ya tsaya tsabar takaici yana kallon su kullum ku rayuwar ku a gudu kuke da tsalle kamar wasu yan biri ko to maza maza ku yi ciki kusa hannun ku a sama.

  Narai narai da ido fadimatu tayi ta kasa motsi a gun ita ko aisha humaira tsaki tayi ta zumburo baki ta juya keya, mamaki ya kama shi ya rasa ma mezai ce musu tsawa ya daka musu kun tsaya kuna kallona ko sena make ku mara sa kirki marasa mutumci.
 
    Ni ruwa zan debo ma da'ada,fa!
Mariya ya kwalawa kira ta fito da sauri tana gani hamma
Dauko bokitin da'ada a dakin inono ki debo mata ruwa ki kai mata kice aisha humaira na sata aiki.
    Tom hamma yusuf.
Tusa keyar su yayi dakin inono yasa suka sa hannun su a sama.
Shi kuma ya zauna kan kujera yana kallon su duk wadda ta sauke ya rakwashe ta a kanta
  Se la'asar inono ta lallaba shi ya kyale su.

Suna fita suka shiga bangaren adda mardiya (matar yayansu ce) tana tuka tuwon alkama dan hamma idirisa yana son tuwon alkama.
  Suka zazzauna aa yan gidana se yanzu
Kede bari adda ai yau mun shiga wani hali
Da me fa?
Hamma yusuf mana
Au ai kun saba se kuyi tayi ai kun ki girma ai zan sa shi ya sa a saku a lalle.

   Suka yi kwal da ido a waje

*2017*
✨✨✨✨✨✨✨
[20:22, 10/01/2017] khairat up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨

*2*

Lalle kuma suka kyalkyale da dariya gaba dayan su harda tafawa suka yi shewa ahayee yerhh!!.
  Mardiya ta kama baki yan banza kun rika ai dama hamma din naku yana nan a daka.
  Da gudu suka kuma yin waje .
   Dakin da'ada suka shiga kuma zaman su keda wuya da'ada ta kama aisha humaira tana duka daldaldal
Ai tuni fadimatu tayi waje tana dariya da kyar aisha humaira ta kwace ta fyalle a guje
  Tayi dakin adda rabi tana kuka adda na daka ta juyo da sauri yaya?
Ba da'ada bace ba ta dake ni
 Kai aisha humaira kin fiya rashin ji wallahi kin fiya kiriniya har se kin kure an miki duka kike jindadi.
  Ta kyabe fuska ta juyo a hasale.
Cikin fada da bacin rai kamar zata make addan
 Addan tace kai ni kike ma wannan kallon.
Wallahi na kara miki dukan.
Ba saiki dake ni ba din in gani.
Tabdi jan tayi kan ta da sauri ta gudu wallahi sena hadaki da isuhu ya min maganin ki ya zane min jikinki tukuna zan ji dadi.

Gidan su amira ta je ta sameta cikin kayan makarantar islamiya zata wuce makaranta tama makara mama na mata fada
  Taga aisha humaira kamar an jefo ta.

 Mama ta kama kai shi kenan Allah ya kawo min ke se kuyi tayi ai amma wallahi se kunje makaranta yanzu in ba haka ba zan sa a kira min yusuf ya zane mun ku wallahi kun fitini kowa gwara ma wannan yaran ya yi ya dawo ko na samu sa'ida a gidan nan
  Amira ta ce nifa mama na shirya to maza jeki dauko kayan ki ku wuce makaranta
  Sum sum suka shirya suka wuce
  A hanya tace ke amira yaushe hamma zai dawo?
Ke har so kike ya dawo?
Eh man kinsan ina matukar san sa
 Tab wannan mugun?
Ke kul kar ki soma ki kuma ce masa mugu
  Hmm kya ji dashi ke kika sani
  Amma ai mugu ne hamma.
  Mintsinin ta tayi tayi kara suka sa dariya.
  Suna gama daukar karatu suka yi hanyar gida suna hira.
A kofar gida suka ga hamma yusuf amira tayi sunkui da kai ta gaid shi
Ya amsa da yar fara'a
Aisha humaira ta sa dariya harda kyakyatawa yusuf ya harareta tayi cikin gida ita kuma
 Amira ta tsaya suka dan gaisa da shi sannan ta tafi gida.

*2017*
✨✨✨✨✨✨✨
[6:25PM, 3/14/2017] Kairat Up: [22:28, 13/01/2017] khairat up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨

*3*
Zaunawa tayi a tsakar dakin da'ada tana kallon ta tana tsinta,to mutniyar ayi hakuri a yi wa da'ada ahuwa kin ji?
Ta zumburo mata bakin ta.
Haba yar lele tawan ki yi hakuri kar a ji kan mu a sa mana dariya.
Sannan ta juyo sai suka kuma sa dariya suna hira ta bata abinci taci.

   Ke yar nan dazi gidan su mutumin ki aka kawo mun waya muka gaisa da wannan yaron
  Wa kuma?
Masdook mana
Ta zabura ta mike da sauri haba hamma ne ya bugo amma ba a ban wayar ba.
To ba kina makaranta ba ?
Kash banji dadi ba mama bata kyautan ba to ya tambaye ni ko ?
Ina fa ya dai bugo mu gaisa ne kan me zai tambaye ki?
Ta zumbura mata bakin ta kai da'ada yana sane ai
 Ta kyabe baki sha kurumin ki ina ji dazu ana maganar za a kai kudin auran sa
Ta mike da sauri wa?
Masdook mana
Na shiga uku
Da'ada da gaske ko da wasa
Ta mata dakuwa kaniyar ki kina ji ko se ki shiga uku saboda auran shi
Da'ada ya za ayi haka ni bazan yarda ba kam wallahi tallahi se an warware
  Ke ni na ga ta kaina yau ni bintu dan ubanki zaki hana ne
 Ta zauna dabas tana kuka da'ada ke ma fa kin san tun ba yau ba ina san hamma kuma shi ne zaki bari a masa aure?
Da'ada ta kama bakinta na ga ta kaina kar ki sake a ji ki ma a gidan nan zaki hana aure ne ke yaushe kuka yi da shi yana sonki zai aure ki?

 Kafin ya koma man da muka hadu dashi a gidan su hajojo da daurin auren hamma isyaku.

Yaushe kuke magana dashi har da zaku yi soyayya  ba a sani ba ?
Da'ada a tambayi amira tasan komai ai
 Shi ne ze ci amanata ya ce wata zai aura
  Da'ada ta ce tabas bazai yi haka ba tunda ya miki alkawari se ya cika alkawarin nsn bs wadda zai aura sai ke
 Dadi ya kama aisha humaira ta yi bacci mai dadi ranar za a bata hamma masdook
Tunda da'ada tasa baki mayafi ta ja tayi gidan su amira tana kallo kuwa ta ce ke zo kiji.
Me zaki zo ki dameni a daran nan?
Ke nayi kwaba fa kuma bana tsoro amma ina fargabar hamma masdook sede ki zame min sheda kawai nake so.
 Me kika aikata?
Fada mata tayi tsalle amira tayi ta dire tace keda wa?ni amira wallahi baki isa ba kar ki soma sa ni a cikin haukan ki hamma masdook din zaki sa ya min tijara ba ban san anyi ba
 Shi kenan ai kar ki taimake ni nima sena ki taimakon ki hamma yusuf ysce yana sonki da zan miki hanya amma na fasa
  Riko ta tayi tsaya kawata zan miki
Ko kefa tayi wani murnushi me kayatarwa na mugunta ta gyara tsayuwarta suka tafa

*2017*
✨✨✨✨✨✨✨
[10:25, 15/01/2017] khairat up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨
4
*na khairat up*
Amma kin san akwai matsala ko idan hamma masdook ji wannan labarin
 Ke kin fiya tsoro ni wallahi akan shi ba abunda bazan yi ba kome ze mun sena aure shi wallahi sena aure shi.
Kallo ta bita dashi kawai tana jinjina karfin hali irin na aisha humaira .
  Komawarta gida keda wuya ta shiga dakin su amma bata samu da'ada ba sai ta zauna a kasan carpet tana jiran dawowar ta
 Bata wani jima ba ta dawo ta zauna kasan ita ma sannan cikin fara'a tace ke kwantar da hankalin ki a kan masdook baza kiyi kuka ba insha Allah kin same shi kin gama daga gun baffan ki nake yanzu nasa aka kira min shi baffan naki da abban masdook din na masu bayanin kudurina kuma ba wanda ya musa min a cikin su kamar yadda nayi tsammani tabbas muhammad ya cika dan halas me tarbiya ya maidani tamkar mahaifiyar sa ko dangin su na asali ban taba ce masa yi ba yaki yi ba tankar ni ce na kawo shi duniya.
  Komai aisha bata ce ba illa ranta fes take jin sa da wannan daddan labarin hamma masdook zai zamto nawa.
Da'ada waccan fa dazai aura?
Kwantar da hankalin ki ke kadai ce bai isa kawo wata ba .
 Dariya tayi na jindadin abunda ta fada ranar baccin dadi tayi.
 ✨✨✨✨✨✨✨

Zaune yake kan kujera yana duba wasu takardu a kan tebur din sa tun kafin ya fara duba patients amma ran shi a bace yake ya rasa dalili kawai Allah Allah yake yi ya samu hutu ya koma gida.

Wayar shi ya dauka ganin tana ringing kuma sunan abban shi ya gani a kai an rubuta
*abbu* dauka yayi da sauri ya ce salamu alaikum,
 Wa'alaikum salam
Ina kwana *abbu* ina gajiya an tashi lafiya
  Lafiya lou ina son ganin ka masdook
Abbu yaushe zan zo
Ko gobe ma kazo
To abbu insha Allah zan ajiye komai nazo
To ina sauraron ka.
Ajiye wayar yayi amma fa gaban shi na faduwa abbu be taba masa irin wannan kiran gaggawar ba in ba yau ba wayar ya dauka ya kira yusuf
 Hello masdook
Yusuf fada min akwai abunda yake faruwa a nan gida ne?
Aa me ka gani?
Kawai naji a jikina akwai abunda yake faruwa nan gida
Aa feel free har yanzu banji wani abu ba kila sai ka zo din se muga
To ina fata hakan ne
Amin
Amma wai har yanzu bska dawo ba.
 Wallahi kuwa kila mu koma tare da wayanan yaran nake son maidawa boarding baffa nake lallabawa ina gamawa zan kaisu munjibir a huta kila su ma su nutsu.
 Haka ne amma wayan na yara ?
Da aisha da amira da fadima da mariya da kulthum
  Gaskiya kam da ka kyauta
 Anyway sai anjima gobe zan shigo insha Allah
Allah baka iko amin.

✨✨✨✨✨✨✨
*2017
[6:25PM, 3/14/2017] Kairat Up: [12:49, 15/01/2017] khairat up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨
*5*
*na*
*khairat up*

Baffa na zaune a falo shi da abbu suna tattaunawa da matan su kan batun da da'ada tazo musu dashi jiya da daddare
Mama tace to me kuke jira na yin shawara?ai bai kamata ta bada umarni ba ace se anyi shawara inji inono
 Ba wai shawara muke nema ba kawai ina ganin kamar masdook zai bamu matsala ban yarda da zancen aisha ba sam sam.

  Ajiyar zuciya inono tayi tace nima dai kawai naji ne amma masdook yaushe zai tsaya soyayya da aisha fitinaniya kunsan yadda basa shiri da ita
 Amma ita aisha tana matukar son sa kuma kunsan aisha humaira ita ce da'ada kuma da'ada ita ce humaira tun bayan mutuwar adda aisha(babar aisha) ta dauko ta ta maidata ta tamkar ita ta haifeta
  Ni bana jin masdook zai ketare maganar mu ya ki ba an riga an zama daya amma gaskiya sai aisha tayi karatu in yaso yanzu a daura auran kamar yadda ta bukata tunda sun ci jarabawar shiga ajin gaba dama yusuf ya zo da maganar boarding meze hana su tafi can ta kara girma da wayo tunda da akwai wadda yake so baza a cuce shi ba sai ya aureta
  Hmm kai ma dai abbu baka ji me da'ada tace ba bata son a mata kishiya.
  Zan lallabata na mata magana har ta sauko amma ai aisha humaira bazata iya daukar nauyin masdook ba.
Haka ne.
Sallamar masdook suka ji a bakin kofar dakin amsawa suka yi ya shigo ya tsuguna suka gaisa gaba daya abbu da baffa suka tambaye shi aiki yace alhamdulilahi.
Abbu yace masdook waye ni a gun ka?
Abbu meya kawo wannan tambayar kuma
Ka bsni amsa
Kai mahaifina ne.
Alhamdulilah da'ada fa?
Bayan ku sai ita
Yayi kyau
To ni a matsayina na mahaifin ka na yanke shawarar daura auren ka da aisha humaira
Da sauri ya dago kan sa gaban shi ya buga ya dinga kallon abbu da sauran mutanen gurin gumi ya tafaso masa.
  Umarni nake baka ba shawarar ka nake nema ba ko amincewar ka ba.
  Abbu ban isa na ki bin umarnin ka ba kuma zan bi ko da banda komai amma abbu nayi wa zainab alkawarin aure kuma yanzu ys za ayi aisha yarinya ce bata da wayan daxata iya dani
   Baffa yace mun sani kuma mun yanke shawarar za a hada da auran ka da wadda kake so kuma aisha zata koma makaranta daga baya ta kuma wayo se ku tare amma za a baka wadda kake so.
   Mama tace wannan hukuncij da'ada ne ba namu ba kuma dole a bi maganarta
  Insha Allah mama bazan ki ba amma aisha humairan ta yarda?
  Kaje kuyi magana da da'ada zuwa jibi zamu san yarda zamu yi
Amsawa yayi ya fita jikin shi ba laka lakwas ba dadi
  Dakin da'ada ya shiga jikin sa a sanyaye ya tarar da aisha da fadima da amira suna yar carafke a tsakar gidan wani irin abu ya tokare masa makogwaro tsabar takaici ya wuce cikun dakin suna gaida shi ba wadda ya amsa aisha murna ya cikata ta mike ta yi waje debo ruwa tayi wanka da kwalliya hamma masdook yazo.
A zaune ya samu da'ada tana jan carbi tana ganin shi ta washe baki tsabar dadin ganin shi zaunawa yayi ya kskalo murmushin jindadi ya gaida ta cikin filanci dan yawance haka suke magana shi da ita.

✨✨✨✨✨✨✨

*2017*
[13:11, 15/01/2017] khairat up: ✨✨✨✨✨✨✨
*Aisha humaira*
*6*
*na*
*khairat up*

Masdook na waje na ka gama min komai tunda kake son abar da nake matukar so kaf duniyar nan ina godewa Allah da ya nuna min wannsn ranar masdook dame zan saka maka ?
Bafan ma ita aishan ta fada min gaskiys cewa kuna soyayya ba ai da ka manta da ita ka auri wata can bare
  Ya dago da kan sa yana kallon ta cikin msmaki ya nanata *soyayya*ni da aisha humaira yaushe?
Da'ada waya fada miki muna soyayya da ita?
Ita man ta fada min kayi mata alkawarin aure tun bikin isyaka ko ka msnta saboda wadda kake so?
Shiru yayi tsabar takaici koda yaji tayaya da'ada zata hada shi da yar yarinyar da ya bsma shekaru wadda bayan gaisuwa ba abunda yake hada shi  da ita ace zasu yi aure.
  Tabbas badan ysna ganin girma da darajar da'ada ba da tuni ya karya wannan shirin
 Amma humaira zata gane kurenta badai shi zsta aura ba harta yi girman dazata hada masa tugu tabdi jam.
Da'ada Allah kara girma ya sanya alheri ni zan je gun su yusuf
To Allah maka albarka amin.
✨✨✨✨✨✨✨
 Ai ko wata atanpa ta saka yello da ratsin pink a jiki ta daura zanin ta da riga yar firit ta caba uwar hoda da janbaki a fuska ta tsaya jirsn sa ya fito ai yana ganin ta wani malolo ya tsaya masa a makogwaro ya dalla mata harara a fuska sannan ya shiga dakin su ta bishi duk da a tsorace take dashi
  Wani kallo daya buga mata seda hantsr cikin ta ya kada ta soma kyarma
 Ni kika je kika ma sharri ko nida ke muke soyayya ko?
Dan uban ki ina wasa dake ni zaki ma karya ai ni kike son aura ko zaki aure ni amma zaki yi dana sanin aurena zaki san cewa ni ba saanki bane ba zaki dandanani zan baki mamaki zaki yi danasanin sanin *Masdook Muhammad dikko*
Shiru tayi ya nunata da yatsa
 Ta zumburo bski oho dai nidai ina sonka kuma sena aureka sede ka kashe ni na yarda in na matu a ce matsr masdook ce da ace aisha humaira kawai kums ksima dole ka soni yadda nake son ka
Mamaki ya ksma shi haka kika ce ko?
To mu zuba nida ke ya fice waje abunsa yana mamakin karfin hali irin na aisha humaira.
Ta soma hararar hanyar da ya bi ya fita.

  A waje yaga su nas da yusuf ran shi duk a bace yake ya zauna kawai dirshan ya rasa meke masa dadi
 Aa likitan birni daga ina kuma waya taba ka?
Nas kaidai bari kaina ya dau caji
Aa likita da kan sa ai se a sha panadol
 Mtsw dadina da kai kennan ka fiya shiririta.
  Ni'imatullahi ya katse su danuwa meke faruwa?
Wai ni yarinyar nan zata ma planning?
Wacca yarinya?
Aisha humaira mana
Meta yi inji yusif ya fada cikin xakuwa shi sa nace zan kaisu boarding
  Mtsw ai in wannsn ne da sauki
Wai zuwa tayi ta fadawa da'ada cewa ni da ita muna soyayya na mata alkawsrin aure
  Ita aisha humaira din
Ita man
Kiran da abbu ya min kenan sun yanke shawarar aura min ita saboda maganar da'ada dole a bita
Tabdi lallai humaira ta hsda ma zafi zainab din fa?
Sai sun duba sun yi shawara.
Lallai an kassara ka an gama da kai me wata aishs humaira zata ms bands tsiwa da rashin kunya da kinji da jawo magana inji yusuf
 Ai wai makaranta zaka kaisu ksn nsn ta kuma wayo da hankali
  To Allah sa haksn shi yafi alkairi
Amin suka fada banda uban gayyar.

   Wallahi sai hamma masdook ya aureni ko kallon shi xan dings yi kullum yana dukana ko namsn jikina zai dinga yanka yana ci sai ya aureni
  Harda hawayen ta
(Son maso wani)
Ta share kukan ta ita knta ta rasa yadda take mugun son sa bayan tasan ita dashi akwai banbamci
✨✨✨✨✨✨✨
*2017*
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨
*7*
*na*
*khairat up*

_ummi_ _hambali_ _ina_ _mika_ _gaisuwata_ _gareki_ _da_ _fatan_ _kina_ _lafiya_.


*zaunawa tayi jugum yau duk hayaniyar aisha humaira shiru kake ji har da'ada da kawayen ta na jajen ta a waje
  Da'ada ta shiga dakin da aisha take ta dafata yar nan yau ya na ganki shiru?. Ana ta cigiyar ki cikin gida.
  Hmm ba komai da'ada kawai dai na gaji ne yau din to ko lafiya?
Ta fara tatabata ko bata da lafiya kuma taji jikin ta ba komai alamar rashin jindadi kawai dai garin ne.
Fita tayi ta barta a dakin.
  Amira ta shigo ita da fadima aminan ta suka zauna gefen ta sannan ta saki ajiyar zuciya kuma hawaye suka zubo mata a fuska daya na bin daya zur zur.
Fadima bintu ta rungumeta a kirji ke menene?
Fadima baya sona baya kaunata
Waye baya sonki?
Cikin sarkewar murya da shassheka ta ce hamma masdook mana
  Amira ta ce aa fa aisha yana son ki man
Aa ta fada tana jijjiga kan ta cikin kuka ni ina son sa wallahi shi ma kuma seya soni
  Anji din amma kema sai kin dage munyi karatu mun fara zuwa makaranta ke ba kya so ki waye tayaya dan birni dashi yasan duniya yaga wayayyu zaki ce wai ya soki a haka muna wasan yara har yanzu?
Hmm ta kyabe fuska inko dan wayewa ce baya sona zan je makaranta kuma zan waye nima sannan na ja masa ajina.
  Fadima ta gyara zaman ta tana dauke kan ta kenan yanzu a fasa auran ko ?
Ta harareta hade da rankwashin ta muguwa bakin yi ya saei danyan kashi kuma se anyi sede ki mutu.
  Aa meye zafi yi hakuri mutuniyar ni na isa in shiga tsakani?
Kin ma isa ?
Suka sa dariya.
 Dazu hamma yusuf yace gobe zashi makarantar yaga abunda zamu bukata a can

Hmm wai da gaske boarding din zamu je?
Eh wacce su husnan gidan baba kabiru suke zuwa munjibir.

Tabdi kice zamu hadu da su ko
Dama ina binta bashin duka goma na wannan wasan da muka yi a soron gidan su mudi ihu suka saka shegeyia haka nake so ai
  *(Kuji fa yanzu take zancen wayewa se zancan ramuwa)*

✨✨✨✨✨✨✨
Yusuf wallahi Allah ina matukar bakin cikin wannan alamarin ni ina zan iya da aisha humaira ta fiya fitina da neman magana dazu fa yar carabke na tarar suna yi kamar ni ni wai ni masdook in auri yarinya yar karama
To ya zaka yi masdook haka Allah ya rubuta so ne kuma Allah na dorawa kowa a kan sa.
Kayi hakuri kaida ka samu ma za a baka wadda kake so

✨✨✨✨✨✨✨
*2017*
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨
*8*
*na*
*khairat up*

Mtsw guy barni dan Allah ku taku me kyau ce kaga wannan aishan se a hankali ai ina jinjina zamana da ita kuma sarai nasan halin ta
  Hmm masdook kenan zaman duniya se hakuri rayuwa tayi tsada ka samu mai son ka ma ai ka godewa Allah wanda ba a son sa fa yayi yaya? Kawai kaja ta a jiki ka koya wa kan ka how to...
Hmm kai yusuf haka ma zaka ce min dawa zan yi rayuwar?wallahi da zuciya1 nake fada maka bana son yarinyar.
 Shiru yusuf ya masa to meze kuma ce masa?
Babu inji khairat.

Wasa wasa kwanan shi hudu a dikko ya koma bakin aiki sa domin baffa da abbu sun sa wata hudu zaa daura auran kuma satin sama zasu fara makaranta ta sakandari a kano munjibir.

   Amina zaune kan kujera tana kallon masdook wanda gaba daya hankalin ta na kan shi hankalin ta a tashe yake da jin labarin da ya kawo mata tsabar takaici kuma kukan yaki zuwa dan bakin hali.
  Ta kalle shi ya yi gum da bakin shi tun bayan fada mata sakon da yayi kuma a gunta sabo wai zai auri wata watan ma karamar yarinya kafin ita itan ma se an yi shawara da danginsa saboda ga me bakin jini mara gata da dangi ita bata ce seta duba ba sai su zasu ce se sun duba
Masdook kayi shiru kuma .
 Zainab mezan kuma ce miki magana na gunki ai
Haka ma zaka ce?
Seda komai yazo mana karshe za ka zo min da wannan labarin marar dadin ji da sauraro a kunne ni bazan iya hada zaman aure da wata ba dan mahaifiyata ma ita kadai ce se ni a kaina za a fara?
To zainab ya kike so nayi ne da rayuwata can ba dadi nan ba dadi kinsan dai ina matukar kaunar ki...
Ya isa ta daga masa hannun ta ya isa kana kaunata ko
Lah shakka
To ka bijire ma iyayen ka ni kawai ka aureni.
Ya mike a fusace in bijire musu saboda ke ?
Ai ina tunanin mun zama daya
 Seya zama me?
Se ya xama na fisu yanzu kamar ya wanke ta da mari haka yaji takaici ya ishe shi.
 Zainab yau kin nuna min cewa ba kya sona
Bana son ka fa kace?
Tabbas duk wanda zai hadani da iyayena makiyina ne
Makiyin ka kenan ni makiyar ka ce?
Sossai ma tunda ba kya son iyayena
Masdook gwara da Allah yanuna min halinka haka zan shiga dangin ka kana nuna sun fini
 Look zainab ya isa is over kiyi naki waje gwara da kika nunan naki rashin tarbiyar tun kafin muyi nisa.
Yq kada kai yayi waje daga gidan
Msmaki ya cika zainab soyayyar shekar biyar ta tashi a mintuna kalilan saboda banzar muhawara marar tushe tayaya iyayen sa zasu fini a wajan sa?
*(Khairi nace tayaya zaki raba da da mahaifi kice budurwa tafi su)*


Zuciyar sa kamar ta fito waje haka ya ke ji Allah ne kadai yasan irin wahalr da zuciyar sa take yi da kyar ya karasa gidan shi zaunawa yayi da kyar ya zauna a kan kujera yana jin jikin sa na rawa kamar mazari
Daga bisani ya dauko ruwan sanyi ya kwara a kansa sannan yaji dadi.

 Wanka yayi ya sauya kaya zuwa marasa nauyi ya kwanta kan gado yana jin wayar sa na ringing amma yayi biris da ita ya dada gyara kwanciyarsa ma daga karshe yasa ta a flight mode .

✨✨✨✨✨✨✨

Gaba daya a rikice suke ba suyi tunanin cewa haka zata kasance ba kuma sai kuka musamman ma da'ada da aisha da kyar aka lallabasu suka rabu ita kuka ita kuka .
  Haka suka tafi makarantar
 Nace da alheri Allah sa suyi karatun.
 **************
Mama ce ta kira numbar din dan nata tilo guda daya yana aiki yaga kiran ya dauka da sauri ys rusuna kamar tsna gurin saboda girmsmata da yake yi
 Babana wai se yaushe zaka taho ne?
Ya sosa kan sa yana muzurai mama zan zo.
Yaushe bana son abbin ka ya fara tunkarar ka tun fa da aka sanar da kai maganar baka kuma leqowa ba fa kuma lokaci ya gabata jibi zaa je masu visiting ya kamata mu sameka a can ko kuwa.
Mama ayi hakuri zan duba kin san aikin namu
Babana gobe fa lahadi
Ai sai yayi shiru mama zata daure shi
Kaga kafi kusa dasu ka daure ka leqa .
Insha Allah mama
Allah bada iko
Amin.

   Sumar kansa ya shafa ya runtse idanun sa.
     Kofar aka bude aka shigo
Ya juyo da sauri yaga waye
Aa nas sannu da isowa
Yauwa man
Nagan ka wani iri lafiya dai ko?
   Alhamdulilahi gajiya kawai.
Ai dole naje gidan ai a kulle nasan nsn kayo
   Wallahi kam nan suka fara hira a tsakanin su ta abokai ta yan'uwa.





✨✨✨✨✨✨✨
*9*

Komai an riga da an kimtsa gaba daya sun kagu suma suga yan'matan nasu da aka kwana biyu ba a hadu ba
Yusuf ys ma motar shi full tank
Da'ada,baffa,mardiya,abbi,mama,inono dasu za ayi tafiyar.
Nas,da ni'imatullahi da adda munnaya da adda munawara suna mota daya lallai yan gata ne yan matan.

Ke kike wani zumudi nameye ne da zaki damu kan ki
Dallsh can da'ada ta fa zasu zo yau ya bazan ji dadi ba mun kwan biyu bamu hadu bafa in ga yadda ta koma ko waye yake debo mata ruwa yanzu kuma oho
  Yar banza kin girma fa suka sa dariya
Fadima tace to Allah sa mutumin naki yazo
  Ke muguwa kar ki damu xai zo dan naji a jikina surely zai zo kuma he  ve to
Suka kalli juna su uku suka sa dariya gaba dayan su
ita kuma ta kulle ta yi musu harara.

Bayan tafiya me dan nisa da gajiya suka iso garin na munjibir tunda ta ungogo suka bi suka kauyuka guda hudu hska yan kanana sannan suka isa garin na munjibir sannan suka shiga harabar makarantar.

Idanun aisha humaira kawai neman abunda take so take amma bata gan shi ba karasawa suka yi ta rungume da'ada da karfi tasa kuka kuma aka tsaya kallon su adda mardiya tace ja'ira ya makarantar ina fata an ladabtar min daku?
Hararta tayi ta wutsiyar idan ta 
Ta ce ina ba a fara ladabtar dake ba tukun
adda ni zamu yi fada fa.

Amira taja ta gefe mrs.overconfidence ina mutmin naki ?
   Ban sani ba ki kwantar da hankalin ki zai zo kuma zaki fada.
  Hmm maji ma gani ai
Tana tsaye kawai taji gabanta ya fadi dum wani murmushi tayi me kyatarwa
Wallahi yaxo
Ai na fada miki se yaxo
Naji a jikina zai zo juyawa suka yi lokacin ya danno kan sa cikin makarantar ya fito daga cikin motar sa parado ya ajiye kafafun sa da takalmin sa me tsada shaddar jikin sa har maiko take yi ga hular nan ta zauna ta amshe shi abun se wanda ya gani fuskar nsn ba walwala amma kamar yana murmushi haka ake gani tsugunawa yayi ya gaida su baffa sannn ya koma gefe ya tsaya yayi gum da bakin sa ya sa hannu a habar sa yana kallon farfajiyar makarantar.
   Tsaye tayi a kan sa tana masa kallo ta masa kuri da idonta.
  Be ma ankare ba har wani lilo take yi na shaukin son da take masa.
  Jikin sa ya basa cewa ana kallonsa.
Ya dago sexy eyes din sa yana kallon ta wani abu ya tsaya masa ya hasala kamar ya doke ta
  Ke me haka zaki min tsaye kina kallo na kamar mayya.
  Hararsa tayi eh din mayyar kace man kuma ai kyau ka mun Allah hamma kayi kyau ka daina kwalliya haka da yawa ana kallon ka.
  Kan sa ya dafa na shiga uku ya fada a ransa wannan yarinyar ko mara kunya
Baki da kunya zaki min tsaye gasu baffa a gun
Ta yamutsa fuska ta matso daf dashi
Keee aisha
Wani dadi taji ya kira sunan ta
Me haka kike yi ?
Soyayya man
Wai dan ina son ka kake min rashin arxuki ko hamma
Ya hade gida kinga mama tasa nazo kuma nazo kin ganni ni zan koma se wata rana ki daina expecting cewa ni masdook zan soki
Ya juya daga gurin ya barta siraran hawaye suka zubo mata a ranta tace
*SO*

✨✨✨✨✨✨✨
*2017*
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨

*AISHA HUMAIRA*

✨✨✨✨✨✨✨
*NA*

*KHAIRAT UP*

*10*

Matsa min mara kunya kawai banda tsaurin ido da rainin hankali ki kalle ni kice min wai ni kike so saboda baki da wayo.
         To so karya ne?
Yayi kamar ya mare ta ni kike fadama haka?
Ta zumburo masa bakin ta tayi tsaki ta juya zaka sani ai in dai nice ban daina son ka har abada kai har gaban abada.
 Tsabar takaici ma magana ya kasa yi ya bita da kallo tayi gaba abunta .

Haka suka gama hirar su sannan suka juya
Masdook yace su bishi gidan shi gobe sa koma dan yamma tayi da kyar baffa ya yarda.
Suka koma.

A gida mama ta kira masdook ta zaunar dashi a kasa
  Kana jina masdook dan Allah kar ka bawa abbi kunya a cikin mutane kasan yadda yake son da'ada ita kuma da'ada humaira ita ce ita yadda take mutukar son ta kuma abbin ka baya son bacin ran da'ada tankar uwar sa haka ya dauketa.

Insha Allah mama zan bi dukkan abunda abbi ke so nima ai ina son da'ada sossai ko bana son abu zan so shi saboda ita
  Jeka Allah maka albarka.
_amin_

Dakin sa ya koma ya kwanta kan gado yana nazari in ba dole ba ta ya zai hada kan sa da humaira?
Basu hadu ta ko ina ba bata da girman da zai rude shi bata da class shi in ba rashin class ba taya mace zata zubda ajin ta tace tana son sa ?
Mtse an gama dani wallahi ita kuma waccan zainab ni zata gayawa magana ta ina zata fi iyayena?
Babu wadda ta isa a doron kasa ya bata mahimmanci fiye da iyayen sa babu ita mata matsala ne a ko ina kullum da tsarabar da suke zuwa dashi.

  Ranar baccin farin ciki tayi aisha humaira taga abun kaunarta taga sahibinta masdook the handsome zan yi karatu saboda shi zan yi komai sabod shi xan nuna masa nima macece me aji me wayewa
  Hamma masdook ina son ka ina sonka ta fada tana rungume fillo din ta.

Tun daga kan nan ta kama karatu ba kakautawa duk wani rawar kai ta rage ta rage yin duk wani wasan banza
    Har suka kare zangon wannan karatun suna shirin komawa gida daidai lokacin daurin auren su ya gabato se doki take amma a wani irin tsari.

Komawar su gida keda wuya aka fara nan nan dasu a gidan
Kowa yayi murnar ganin su a gida yadda suka samu nutsuwa a tare dasu ba karamin mamaki ya bawa su inono ba.

  Kwana uku a tsakani da dawowar su aka fara maganar auran masdook da humaira inda baffa ya tara jama'a maza kawai bayab sallar juma'a karfe biyu da rabi aka daura auran
Masdook da aisha humaira kan sadaki dubu ashirin sabida albarkar ake nema .

 Aisha humaira da jin wannan dadadan albishir ta shige uwar daka ta kwanta daga bisani tayi alwala tayi sallah raka'a biyu dan godewa Allah daya cika mata burin ta bazata taba manta wannan rana ba ranar juma'a a watan janairu aka daura auran ta da habibin ta abin alfaharin ta
  Ta ys zata manta wannan rana?
Babu kam inji aminiya ummu arif.

Masdook dama ana daura auran befi hour daya a garin ba ya koma ksno da abbi ya tambayi dalili yace saboda aiki ba a wani bashi hutu ba ya fada ne kawai dan ya nesanta kansa kar a ga rashin farin cikin sa da wannan auran.

Hajiya da'ada ta dinga raba alawa da goron biki na murnar auran jikokin ta guda biyu.

_muje_ _zuwa_ _dai_ .





*11*

Hutun mako na karewa suka wuce makaranta amma gaba daya aisha humaira hanklin ta na kan masdook tun bayan daurin auran be kuma zuwa ba kullum in sun yi waya da baffa ko abbi ko su mama yace aiki zai zo ko da makarantar ne amma kasan ranta tasan ya fada ne kawai karya yake yi ita ce baya son gani kawai.

Masdook,yusuf,nas,ni'imatullah,hanif zaune a tsakar falon masdook suna hirar bayan rabuwa
   Kai ango haka ake yi sai ka bace daga murna?
  Hmm kai ne kake ganin abun murna a cikin wannan auran
Auran alakakai.
   Kai mutumina baka da kunya da kirki muna nan kake ci ma yar'uwar mu mutunci ko
   To ace ban da hadi da ita man
  Aa meye zafi?
To ai karshen cin muntunci kenan
 Ni'imatullahi yace dana san da haka dana shiga na fita da fadanci na karbi auran aisha humaira
  Kallon shi kawai masdook yayi ya kyabe fuska ya dau lemo me sanyi ya sha ya ajiye ka makara kuma ba .
  Me aibun humaira masdook kai ko.
 Tana da kyau
diri
Ido hanci zukeke
Ga gashi ga haske irin matqn nan ne masu kyan jiki da tsari tana da fara'a in ma yarinta ce ai zata daina lokaci ne kaima fa kayi nagani
   Yusuf yace amma hanif kai dan iska ne kai kuma ka tsaya ana tanka ma zubi da tsarin matar ka ko kayi shiru ai da ni ne da tuni na make masa baki yayi jini
 Aka sa darya ban da ogan ya sha mur yana wani nazari na daban shi kadai yasan me yake tunani se wanda yayi shi (Allah).

Ku kuna ta ma humaira campaign inji yusif ku barshi man ai ido ke gani shi be hango ba amma ina tabbatar muku da cewa zai dawo yana a masa sulhu in ya fada tarkon yar mitsilar yarinyar da ya raina.

Fatan ka kenan yusuf?
Sossai ma.
To xamu gani ai inda rai da lafiya ba
 Yes we shall see.

   *BAYAN SHEKARA UKU*

Wasu siraran hawaye ke yawo kan kuncin kyakyawar fuska me dauke da murmushi kullum a yau kuma hawaye ke zuba kamar bazai kare ba
   Ta gefenta ta riko hannun ta tana rarashin ta haba kawata haba ban san ki da haka ba ni kawata jaruma ce wadda tasan jaramunta da dauke kai kin hakura har shekaru uku balle yanzu kuma?
  Hmm bazaki gane ba so dafi ne me wuyar warkewa so in ya kama ka baya cika ka so wuya ne dashi so nauyu gare shi a zuciya musam irin wanda nake yi *son maso wani* amira only my Allah knows yadda nake son hamma amma na rasa mesa baya sona har bakin jini na ya ksi haka amira da za a kini?
Me aibuna na gyara?
Me nake yi mara kyau fada min na gysra?
Ta fada tana jijjiga ta tana kuks fada min amira fada min.
 Na gaji wallahi Allah na gaji na kasa sukuni
Duk sanda na runtse idanuna shi kadai nake kallo shi kadai nake gani a ko ina na kasa cire shi daga raina am getting mad amira zan zauce
  Rungumeta tayi haba kawata ki daina damun ksn ki insha Allah komai zai zo karshe komai yayi farko ai zai yi karshe ki daina damun kan ki focus in ur education ki bar hamma besan me yake loosing ba
 Kiyayar tayi yawa amura good three years ace ban sa shi a idona ba
   Na sani amma ki kara hakuri shi ne ribar zama na duniya ki kara hakuri kin ji
 Kema ur tym will come zaki ce na fada miki .

 Allah sa amma zan koya wa kaina share alamuran sa a zuciyata.
  Ko kefa ki daina kuka kawai ki min murmushin nan naki dake nunan cewa yes wannan ce *Aisha humaira* ta
  Murmushi ta mata me kayatsrwa
Point dinta ya loma ya koma ciki sossai karamin bakin ta ya kuma tsukewa ta share hawayen ta sannan tace so ba karya bane ill make it
yes zaki iya.


✨✨✨✨✨✨✨
*2017*
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨

*AISHA HUMAIRA*

✨✨✨✨✨✨✨

*12*
*na*
*khairat up*

Aiki ya gama kacame masa a office bashi da hutu sam sam
 Ga wani gumi da yaji yana zubo masa har rawar jiki yake yi saboda ciwo
  Drower ya bude ya dau maganin sa yaga wayam alamun babu kenan tsaki yayi ya juya dan dauko wayarsa da kyar ya iya dauko wayar ya danna number abokin sa nas
 Hello nas
 Ya akai masdook
Nas dan Allah kazo office ko da lemun tsami ne
Ni ina zan ga wani lemun tsami ?
Ban sani ba kawai i need it.
Yq kashe wayar ba tare da ya kuma jin meze ce ba
 Nas dake kwance a quters ya mike ya duduba ko da akwai a fridge din sa yaga bsbu tsaki yayi ya dau mukuli yayi waje
  Masdook ko ciwon ciki sossai ya ksma shi ga fanka ga ac amma duk da haka gumi yake yi ya kasa sarrafa kan sa.

Kasuwa ya je ya samu lemun tsami ya yi asibitin.
  A yadda ya same shi ba karamin kaduwa yayi ba ya yi saurin tallafo shi aa masdook jikin ne har haka?
  Ina lemun ?
Ungo ya bashi ya dan lasa a bakinsa ya kuma zuqa ya kwankwadi ruwa ya kwanta a kan kujera.

Yayi ajiyar zuciya.
Masdook wai kana son kan ka kuwa?
Ban gane ba nas
Masdook kasan cewa halin da kake ciki ya kamata ka samu partner a kusa.

Hararar sa yayi ya juya masa baya kar ka soma nas kasan bazan iya kiran wannsn yarinyar ba dan ba abunda zata iya min bata kai ba kuma ba zata kai ba.

Ok naji amma zaks iya samo wata matar ko ka aura wadda kake so.
  Ina zan samu kawai nas na fawalawa Allah komai

To Allah kiyaye amin.
Nagode na taimakon da kayi kuma kar ka fadawa ko da yusuf ne
  Ok naji ta wuce.

Amma in fadama wani abu?
Uhm kawai ya fada.
Ka yi reconsidring din dangantakar ka da aisha humaira aure ba fa wasan yara bane kuma kana bukatar ta tunda an daura auran ka daure kayi kokarin ganin kun zama daya kaga tana sonka kar Allah ya ksma ka da hakkin ta.

Hmm nas nagode sossai .

     *makaranta*

Sun shiga ss1 yanzu a science class amira da aisha suke.
  Komai ya sauya musu domin nutsuwa taxo musu sun rage wannsn shirman na yarinta musamman ma aisha humaira da ta kara girma.
 
  Kullum da son shi take kwana take tashi a ranta amma hakan besa ta daina karatu ba illa ma da ys bata kwarin gwiwar yin karatun a ganin ta dan bata da ilimi da wayewa yasa baya son ta shi sa take ganin idan tayi karatun zai so ta.

   *****************

*a gurguje kuyi hakuri ina dan yin labsrin da sauri ne hakan ya kasance ne saboda wasu dalilai da dama*
                  ✨
**********✨*********
                 ✨
Tafiya take yi kamar tana tsoron taka kasa hannun ta rike da wata iriyar jaka ta gayu rataye a tsintsiyar hannun ta
  Tayi irin daurin nan na zamani me hawa hawa ta ci ado tasa irin takalmin nan me tudu ta saka
 Gefenta amira ce wadda na dinga kallon su yadda suka yi kyau suka canja gaba daya kamar ba jikokin da'ada ba tsabar nutsuwa.

   Fadima ta riko hannun *aisha humaira* kinga sis mutumin ki ya iso fa
  Dagowa daya tayi ta masa kallo daya ta maida kan ta kan wayarta gaban ta bugawa yake yi amma ta basar zuwa ysnzu ta san cewa hamma masdook bazai sota ba ta koys wa kanta kokarin share shi ita ma kila nauyin zuciyarta ya ragu.
  Hamma yusuf ya yafito ta da hannu bata gani ba fadima ta tabota hamma yusuf na magana
  Tsaki tayi tana taunar cingum kamsr a kan ta a ka fara cin cingum.

  A hankali ta karasa gurin da suke inda kamshin turaren ta ya musu sallama
  Gani hamma
Ungo ya mika mata leda gashi soveniers ne kuyi amfani dashi a gun dinnar din ku bawa mutanen ku.
 Tom hamma angode
Amma kina ji ?
Eh
Ki fadawa amira ta dan koma daga ciki mana kafin anjiman ban son ana kalle min ita
  Murmushi tayi to hamma angama a mana afuwa mun yi laifi
 Ta juya kenan yace baki gs masdook bsne?
Na gan shi ta kara gaba dan inta kara tsayawa zata kasa daurewa.
  Masdook besan inda zai sa yanayin da ya shiga ba amma yasan cewa lallai yaji wani abu a tare dashi.

Mutuniyar fa ta koyi halin naka
Ni ina ruwana da ita?
Kai ko kake da ruwa
 Hmn kai ka jiyo
Hhh kai kam ka ksms ka rike ta ka kyaleta mana masu so su aura
  Wani kallo ya masa yana gyara tsayuwar sa
  Ni na rasa tsayuwar me suke yi ma a waje gaba dayan su .
Ni'imatullahi dallah kora yaran can cikin gida
Wane yara?
Gasu can man
Ya kalli yan'matan yayi dariya a ransa ysce wannan masdook da manyance yake wallahi.

✨✨✨✨✨✨✨
  *2017*
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨

*13*
*na*
*khairat up*

Wai ya zaka hana yanmata sha'anin biki ina aka taba kora daga harkokin biki in ba a gunka ba masdook
  Hararsa yayi sannan yace ni da ma...
Se kuma yayi shiru
Karasa mana masdook matar ka ko?
Ban ce ba kar ka kaini inda ban je ba
  To ma gani dai masdook .

   Bayan magrib suka nufi gurin kwalliya su hudu harda amaryar
   Inda sun sha ado da kwalliya se walkiya suke yi
  Kayan jikin su iri daya sun sha dinki ya kama jikin su dake fitet gwon suka sa hill da roses 
 Ba karamin haskawa humaira tayi tadan dosana mayafi kan kafadar ta
  Da karamar purse a hannun tq kalar sarkarta da takakmi

  Angwayen sun sha ado suma suna jiran amaren cikin mota da aka faka guda uku .

Masdook ni'imatullahi da nas sune ke jan motar jiran su kawai suke yi su fito su tafi hall din dan su ake jira a gurin.

   Fitowar su keda wuya masdook ya maida hankalin sa gaba  daya kan humaira gsba daya ta tafi da imanin shi amma a fuska baxaka gane ba ya ci kunu ya sha mur ya bata rai
 Bude motar yayi ya shiga a tunanin sa zata shiga motar sa ne sede abun mamaki motar ni'imatullahi ta shiga gidan gaba fadima ta shiga motar da amaryar da angon suna motar masdook.

Haka aka yi tafiyar.
   Isar su keda wuya kowa da wani a gefen ta suka shiga cikin tsari suna xama ya samu gu ya zauns har kan sa ya fara juyawq ma shi saboda hayaniya banda matsayin yusuf a gurin sa ai ba abunda zai kawo shi gun nan.

Can aka saka wakar kujerar tsakar gida ta ado gwanja kar kusu kuga yanmata da maza yadda suka hade suna cashewa.
   A xaune take amma kidan ya tafi da ita bata ma san sanda ta shiga filin rawar tana cashewa wani hadaddan guy ya mike cikin isa da salo yana mata liki a jikin ta ganin ya nace mata yasa ta gyara tayi waje ta koma gurin inono ta zauna
 Inono tace ke kam anyi ysr kaniya kin shiga rawa kamar wata budurwa kuma mijin ki na nan
  Inono ayi hakuri .
 Kiranta fadima tayi mikewa tayi ta isa gareta aka sha gabsn ta dagowa tayi da sauri dan ganin waye wannan guy din ne ya sakar mata murmushi tsadadde
  Kai tsaye yace ina son ki sunana *ADNAN MUBARAK CIROMA*
Ina fata zaki ban hadin kai mu sasanta ksn mu waya sani ko mune next za ayi...
  Yi hakuri bawan Allah ina da aure
  Haba dai ki bsri mana ai baxan yarda ba cewa kina da aure dan ki yafice ksn ki daga gareni ni kuma na gani ina so.

 Wallahi ina da aure ga mijina ma can ta nuna masa masdook wands tun daxu yake kalllon su ya sha mur ya dauke kai kamar baya gurin amma basarwa yake kawai ya rasa dalilin da ya sa ran shi ke baci kan yarinyar da baya so kawai abu daya ya ke masa yawo a kwanysr sa
*ina sonka kuma dole ka so ni*
Ya girgixa kan sa yana cewa *no* bazai yuwu ba.

Kinga zo dan Allah zo mu zauna kinji mu fuskanci juna in ba haka ba zan biki duk.inda kika shiga Allah.

Jin haka ta tsorata sannan ta zauna kan kujera ya zauna shima
Ko kefa sunan ki fa?
*Aisha humaira*
Nyc
Dan Allah kice kina sona zaki aureni kinji wallahi ban taba haduwa da macen data sacen zuciya cikin yan lokuta ba kamar ki (love at first sight)
Nagode adnan amma ka makaro ni zuciysta mutum daya keda ita daga shi babu wani har abada ka fahimce ni ka yarda kuma duk wsnda zaka tambaya a nan matsayina zai fada maka cewa matar aure ce
  Oh God nima mijin aure ni naga alama sona ne ba kya yi.
  Murmushi tayi hmm aisha humaira mutum daya zuciyarta tske so take kauna kamar yadda uwa ke san danta haka nake son sa ba me maye gurbin sa a raina ina fata ka fahimta.

  Nayi rashi hummy nayi rashi amma ...kawai mutum suka gani a kan su ya tsaya yadan rankwafo ya ce bawan Allah ko zaka iya bani aron matata?in kun gama gaisawa ?
  Am sorry fa kayi hakuri
 Hannun ta ya kama ya yi waje da ita inda ba hayaniya. 
  Cikin mota ya turata ys kulle da key yayi gaba abunsa.
  Ta dunga bugawa hamma ka bude min kofa zaka rufe ni ksmar wata fursuna ka bude open the door.

Komawar shi keda wuya gun adnan ya koma ya nuna sa da yatsa kayi na farko kayi na karshe ksr ka kums ko a hanys ne ka nuna kasan matata ya kada ksn sa ys shiga cikin hall din sossai wajsn su nas ya zauna
    *Ikon Allah* *se* 👀
✨✨✨✨✨✨✨
*2017*
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨

*AISHA HUMAIRA*

✨✨✨✨✨✨✨
*Na*
*Khairat up*
*15*

Nas ya dafa shi ya dai man
Ba komai.
Da kyar ya tsaya aka gama kammala partyn
  Humaira yake nema gaba daya idan shi na neman ta amma be ganta ba
Nadiya ina humaira?
Sun tafi a motar hamma ishaq .
 Yyi jim ya gyada kai ya fice ba wacca ya dauka a cikin yanmatan harsu inono din be bi ta kan su ba.

Komawarta gida keda wuya ta yi wanka tayi sallar isha'i ta sa wasu rikitatun kayan bacci dake mutuniyar bata son zafi ko takura musamman manyan kaya ta baje kan gado ana hira amma hankalin ta na wani tunanin na daban dadi take ji hamma masdook ya fara kula da lamarints amma haushi daya take ji da beyi ba sai yanzu daya ga ta girma ta sauya kama mtsw dan rainin wayo kawai
 Kedawa ke kuma hajjaju?
Ban sani ba magulmata
Maida wukar sis bani na kar zomon ba rataya akw bani
Suka sa dariya gsba dayan su.
   Har bacci ya fara dauketa
 
  Shigowa yayi cikin kananun ksya ya canja kaysn sa ya shiga dakin da'ada ya zauna suka gaisa da'ada ina humaira?
Humaira tayi bacci yanzu ai dan tun daxu ta shirya ta kwanta kasan gajiyar biki.
 To dama zan fada mata wata magana ne
  Amma tunda ta kwanta bara na fada miki ki sanar mata kar na ganta gobe ba mayafi gun bikin nan kuma kar ta kuma tsayawa da wani kato

To ayi hakuri insha Allah zata kiyaye
  To seda safe
Allah tashe mu lafiya amin.

 Dakin ta leqa taga tayi bacci amma sauran na hira ku bazaku kwanta ba ku huta ga wani taron gobe zaku yi.

To yanzu zamu kwanta.

***************
 Da asuba ta tashi da matsanancin ciwon ciki da kai ta dinga kwarara amai gashi ta galabaits hankalin da'ada ya tashi ta kasa sukuni yar lele ba lafiya.
  Mutsumutsu ta dinga yi a kasan bandakin jini ko ya bata  mata jiki rabia ta kira wo inono aka taron mata a kai.
   Gaskiya tana wahala yarinysr nsn duk wata ace se mutum yayi kamar ya mutu
  Masdook na dakin sa yaji ana hayaniya fitowa yayi dan jin ba'asi 
  Meya faru kuma?
Humaira za a kai asibiti 
 Humaira kuma ?
Meya sameta
nima ban sani ba gashi dai zasu shiga mota da ita
  Key ya zara yayi waje da sauri amsarta yayi ya sa cikin mota ta gama galabaita bata gane kowa a gun
Numfashi sama sama take kawai idanta ys lumshe ta suma a gurin.

Rudewa mama hajja tayi shi kuma ya kara gudu har suka isa asibitin aka shiga da ita emargency
   Sai zarya yake yi a waje ya kasa zama gu daya mama hajja da inono sun zauna jigum.

Jin kadan likitan ya fito ya ce wani ya biyo shi office din sa ya zauna yana kallonshi
  Gaskiya tana fama da ciwo a cikin ta wnda shi yasa take shan wuya wajan aladar ta duk wata
  To dr.me za ayi yanzu ?
Ina tunanin better case ayi mata surgry a cire mata abun insha Allah komai zai dawo normal
 To dr yaushe za ayi aikin?
Anytime from now in kun shirya
Ok
  Amma waye zai yi siging na yardar op din?
Ni
Wa kake a gunta
Mijin ta ne
Ok to anjima ka dawo munyi admiting nata
ai kasan proccess din komai dan se yanzu na gane ka dr.masdook muhammad diko
  Murmushi yayi kawai ya fita.

Kai ya akai me likitan ya fada.
Cewa yayi za a mata aiki kar ku damu muje na sauke ku a gida zan dawo anjima
  Aiki kuma masdook meya sameta hska
Bayani ya musu a nutse yadda hankalin su baxai tashi ba
  Ya kai su gida ya yi wanka again ya debi kayan ta biki dai ya tashi a alhinin yar so yar lele aisha humaira ta da'ada matar manya masdook
   Haka aka daura auren ba wani jindadi dan dai ya zama dole ne da dagawa za ayi ma
✨✨✨✨✨✨✨
*2017*
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨

*AISHA HUMAIRA*

✨✨✨✨✨✨✨

*na*
*khairat up*
*16*

 Yana kimtsawa ya koma asibitin bata farka ba har zuwa wannan lokacin
Kan kujera ya zauna inda ze dinga ganin movement nata
 Kusan after minti uku seya duba plus din ta sanan ya zauna
   Wajan magrib bayan anyi sallah dr.isa ya fara shirya aikin da zasu yi
  Hannu masdook ya sa aka shiga dakin op din da humaira shi ma bin su yayi dan is allowed .

   Banda baffa da abbi da baffa kabir ba kowa a asibitin.

Masdook ne ya fito yana cire gloves nurse na amsa ya dan sha mur
 Baffa ya ce ya dai?
Alhamdulilahi an samu nasara hutawa take yi an maidata dakin hutu.

To masha Allah alhamdulilahi har naji dadi a raina bara na kira su da'ada na sanar musu ko hankalin ta ya kwanta dan ta fi kowa damuwa dan humaira komai ce ta da'ada.

Hmm a ransa yace baka ji tawa zuciyar ba abbi da ka tausaya min fiye da kowa.
    *

Washa gari ta farka lokacin fadimatu ce a dakin su msma na waje a zaune kan kujera masdook kuwa ya komq gida ya dan kimtsa jikin sa ya huta sai ya dawo
  A hankali tw kira sunan Allah tana kokarin mikewa fadimatu ta yi wuf ta mike ta yi wajebdan kiran mutan gidan.

Da sauri suka shiga dakin gaba daya dan ganin ta
  Tayi fayau ta rame cikin kwana daya cuta da wuya (wayanda basu da lafiya Allah yw basu lafiya masu shi kuma Allah ya kara musu).

Ya gama shiryawq kenan ya dau mukuli ya fita yaji alamar sako a wayar shi dubawa yayi da kyau kuma fuskar sa dauke da mamakin ganin sakon da number din
   *ya kake habibi na ina ka shiga ka manta dani masoyina ka manta da baya ka dawo mu fara sabuwar rayuwa nasan ni kake so ba wannan yarinyar ba*
  Tsaki yayi ya cigaba da tuki abun sa

    Haka ya tsaya a supermakert ya yi yar siyayya su yougurt da abubuwan kwadayi dan yasan humaira amma be siya za'ki ba dan yasan larurar ta.

    *ya zaka min biris duk yadda nake son ka ka manta baya nasan nayi kuskure amma ka yafe min ina kewar ka*

  Sitiyarin ya buga yayi tsaki
  *ban san ciwon kai kar ki kuma damuna ina wuce guri na wuce har abada baki isa komai ba yanzu a gurina ki fara koyo daraja iyayen wasu tukuna sannan na ga ko zan iya kara ki rayuwata*

Tana kwance a kan gadon ta taga sakon ya shigo dubawa tayi cike da mamaki tabdi jan lallai masdook ni xaka  wulakanta?
  Dani kske zancan.

**
 Hankalin ta kawai masdook take son kalla shi take son gani ko taji sanyi a ranta
  Soup inono ta bata a baki ta amsa tana sha ta shagwabe mata fuska inono ni bani son wannan abun
  Ki bani abinci me kyau naci
Uwariyo ki sha soup kiji dadi a jikin ki abinci me nauyi ba yanzu ba zuwa gobe ko jibi
  Kai ni wallahi bani son wannan gwara yougort da dan chips
  Bakin kwadayi ysr banza ki sha kina jina ko
   Ana haka masdook dikko ya shigo
 Lumshe idanun ta tayi dan kanshin turaren sa da ya ratsa dakin 
  Gaisawa suka yi da ysn dakin sannsn ya ajiye ledae hannun shi .  Ya me jiki kuma?
Jiki alhamdulilhi da sauki gashi zata fara aikin za a dora daga inda aka tsaya.
  Me take so kuma?
Zaqi man
 Nifa inono yought nace ba zaqi ba ki barni na sha ko suger free ne
 Ke kika san wani sugerr me oho miki
 Ta zumburo bakinta hamma pls ka sa su bani ban san soup

Fadima!
  Na'am hamma!
Bani ledar nan
Dauko masa tayi ta bashi ya dauko yought din zaunawa yayi kusa da ita ya dinga batq a baki
 Fadima ta kalli amira suka kanne ido daya a tare suna murmushi kasa kasa.
   Ya dan xubo mata gefen baki ya sa hanki nasa ya goge matq bakin
  Inono da mama suka fita daga dakin haka ma amira da fadimatu suka bar dakin suma.

  Hannun sa ta rike alamar ta koshi
  Ido ya bude mata ya kuma sa mata a baki
  Ta karba da kyar tana gyada masa kai alamar aa ta koshi.

Kinga bayan zama a nan ina da wasu ayukan fa ki karba kawai ki koshi ina da uzuririka da yawa dazan yi.

Hmm ta fada masa kawai tace ni na koshi nima ban ce ma ka zauna ba a nan kana iya tafiya ba rike ka nayi ba.

Kallo ya bita dashi na mamakin humaira sossea ta canja masa ko dama can haksn take garin ya mike ya zubar a kan rigarsa tsaki yayi ya shige toilet
  Dama ya bar wayar sa a kan gadon
 Sako ya shigo kamar karta dauks se ta dauka ta duba
  *pls masdook nace ka yafe min wallahi na tuba ina son ka zan iya zama da kowa ma a ksn ka zan iya zama da iyayen ka da so called matar ka*
  So called?
Ni kenan lallai ma wannan koma wace zata san cewa hamma masdook nawa ne ni kadai ba wadda ta isa shiga tsakanina da ita
Num tayi copying a brain din ta tayi sauri ta qjiye masa ta kwanta abunta
 Haka ya fito ya karqci kallonta sannan ya fita.

✨✨✨✨✨✨✨
*2017*
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨

*Na*
*Khairat up*
*17*

Juyowa tayi a kufule tana kumbure kumbure abunta tsaki tayi yafi a kirga ta riga tasan matakin da zata dauka kan wannan mayyar dazata ruguza mata rayuwa tun kafin ayi zaman auren ma.

Kwananta biyu a asibiti aka bata sallama taso taje kai amaryar amira amma dada ta hanata zuwa cikin yan kwanaki ta murmure tayi fes da ita ta dada cikowa
Ranar da yamma suna zaune a kan tabarma ita da fadima da ummu jamila suna hira
 Ta dau wayar ta wannan number ta danna tq kirawota harda shigewa uwar daka inda ba hayaniya.
  Hello!
Ba rokon ki nike son yi balle tambaya ina miki warning ne cewa ki tabbata kin rabu da mijina ki daina shiga harkar sa babu ke babu shi kina shiga min rayuwa kar ki kuskura ki kuma kiransa ko da a waya na mun gode da gaisuwar ma
  Ke dakata waye mijin naki?
*Masdook*!
Ohh kece dama banzar yarinyar data yi sanadin *(a sanadin ki littafina na gaba insha Allah)*

Ke kikayi sanadin rabuwata da masdook amma ki sani sena shiga rayuwar ki ta yadda bazaki iya fita ba sena ruguza farin cikin ki ta yadda zaki daina dariya ki manta yadda ake yinta masdook nawa ne nawa ne kawai ni kadai.
   Shi kenan ni ina da wani karfi guda daya kinsan me wannsn karfin nawa?
  Shiru ya biyo baya ok barq ma kawai na amsa miki
   Karfin Aisha humaira masdook shi ne karfina kuma matukar ina tare dashi matukar ina numfashi to da son masdook nake numfashi ko wanne dakika da second duk wani jini dake yawo jikin aisha humaira da son masdook yake diga tun bansan so ba nake son hamma masdook shekaru goma sha daya ina *dakon son sa*
A raina amma bsn bari yq kubuta min ba to ta yaya zan bari keda kika shigo rana tsaka na bari ki amshe shi a bagas?
  Na fada miki ki nisanta kan ki daga mijina snatcher kawai.
Ki nemo naki mijin masdook ya mijin aisha humaira ne.
Tq kashe wayar tana masifa kawai mutane su dinga bin mazan wasu suna damun rayuwar su ni da na zaunadashi ne ma yace yana sona ai da da sauki
  Kuka kuma ya zo mata ta juye hawayen ta idan abun ya cita wata ran tayi ta kuks ita kadai tq rasa wanne irin so take ma hamma masdook wanda shi ba haka take a gunsa ba.
  Hannayenta ta daga sama ta kai kukan ta ga ubangijin kowa da komai dsn shi zai yaye mata shi kadai zata dogara dashi ba mutum ba ya Allah ka dora masa sona yadda ka dora min nasa
Wallahi ina son hamma masdok
  *(so me wuyar sha'ani)*







*18*

Wayar ta yarda a kasa ta tarwatse a gun kan buuu ni wannan yarinyar zata karqntawa karatun rashin kunya da wulakanci lallai ta nunan ita din meson masdook ce amma nima nayi alkawri guda daya sena shiga rayuwar su sena tarwatsa su sena yi kace kaca da wannan soyayyar .
   Ta zauna tana saka abunda zata aikata mata ta huta a rayuwarta taji dadi ko bata auri masdook ba seta raba ta da masdook .

    ****

Kowa ya watse gidan ya yo tsit cikin wasu kananan kaya ya fito se kamshin turaren sa ke tashi ta ko ina ga tsadaddan takalmi ya saka ya dauko jakar laptop nasa ya shiga dakin dada dan ya mata sallama wucewa zai yi kano.
 Dada zan tafi !
   Aa tun yau masdook?
Wallahi na bar aiki fa da yawa kin san aikin namu
 To Allah kiyaye hanya
Amin.
Dada ina humaira?
Ina ga tana dakin ta
  To bara naje mu gaisa na wuce
To to
Ya shiga dakin humaira tana bandski lokacin daya shigo seya ji dakin ya masa dan shi meson kamshi ne dakin ko banda kamshi ba abunda yake tashi kums kal dakin ba kazanta .
    Tana waka ta fito daga toilet din
   *yanzu ni da kai ba shamaki bari ja da baya kar mi haka*
Tsayawq cak tayi tana mamakin ganin mutum a gurin
   Zata koma ya daure fuska
Ke ban san hauka mezan gani a jikin ki dazaki gudu a banza in kin koma ma zan fada miki ne zan tafi yanzu in akwai abunda yake damunki ki fada min ba sena tafi ba jarabar taki ta motsa miki bana nan kuma
   Kallo ta bishi dashi kallon me kake nufi ?
Kallon wacca jaraba kuma?
   Kin sa min ido kamar mayya kina kallo ina jiran ki ina da ayyuka masu muhimmanci da suka fiki fa
  Ta hararesa ba abunda nike so Allah kiyaye hanya ya kiyayeka daga sharrin masharata kawai ta fada
 Ya bita da kallo kawai yadda yaga jikinta me matukar daukar hankali
   In ka gama kana iya fita zan sa kaya ne ban san ana tsaya min a ka ko a takure ni da kallo.
  Kunya ta kama shi yayi waje da sauri abunsa.
  Ta window ta leqa har ya fice daga harabar gidan gaba daya.
  Zan yi kewar handsome look naka.

****
Wai ni baffa wannan yaran su yaushe zasu tare lokaci yayi fa da ya kamata masdook yace wani abun
   Haka ne amma tunda banga ya motsa ba shi yasa bsn yi magana ba
Amma nags yarinyar zata fara makaranta a can buk idan lokacin yazo ba sai kawai su karata su biyu ba.

Haka ne Allah ya taimaka yasa ayi a sa'a
Amin.

   Ni fa dada yau gidan amira zanje
Ni bsn hanaki ba amma ki tambayi mijin ki
 Wai kice in tambsyi mijina yana ina dazan tambaye shi?
Kawai ki bani kudin mota ko na je gun baffa da abbi ya bani.
  Ni ba ruwana kinsan halin masdook yana jin kin fita zai min wannan aikin nasa
To ina ruwan sa da fitata?
Ban sani ba
Wallahi dada sena fita kawai ki ban kudin mota kinsan banda kudi
Nima banda shi mara mutunci
Dada dan Allah ki ban wallahi na riga nayi niysr zuwa kuma na fada mata naga da fitar nake ba tambaye shi ba sede in tambaye ki kuma ki barni se yau.

   *so ba shi ne se mutum yana son ka ba ya kasance so so yana faruwa ga kowa ko ka shirya ko baka shirya ba idan Allah ya riga ya shirys maka ba yadda zaka yi one has to be self content with what he have*

✨✨✨✨✨✨✨
*2017*
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨

*na*
*khairatup*
*21-22*

Ba wani jimawa suka yi ba suka sauka a katsina gouruba road
   Wayarta ta zaro ta kira num aminiyarta
  Hello amira
Hello sis kina lafiya?
Wallahi alhamdulilahi ina kalau ya mijin naki da gidan ?
Wallahi komai alhamdulilahi
  Kizo waje man ki bude min kofa
  Kee sis ban san tsokana fa
Shi kenan bari mu koma tunda baki son ganin mu
Aa ina zuwa mayafinta ta zara tayo waje tana budewa taga sis dinta ai da gudu ta rungumeta tana ihun dadi
Wayyo Allah na yar'uwa shigo daga ciki
 Hamma kamal sannu da zuwan ku naji dadi sossai yau kune a gidan
  Dama ina ts zaman kadaici kai amma naji dadi
  Suna xama ta tara musu abun makulashe a gaban su
  Ya karfin jiki kuma?
Da sauki wallahi
To masha Allah.
 Hamma sannu da zuwa kune na farkon zuwa gidana
  Uhm lallai kam ina hamma yusuf din
Ya dan fita amma nasan yanzu ya kusa yana hanyar dawowa
 To ai shi kenan.
Amira ta kasa zama yi wannan hada wancan ta gama hada musu abu mai dadi sannan ta zauna
   Jim kadan hamma yusuf ya dawo suka zauna suka gaisa ya yi cikin daya falon da hamma kamal suk barsu a anan.

Kee sis haka kika kara fresh cikin kwana biyu kawai me hamma ya baki haka?
Hmm krdai bari kema zaki je gurin
  Wallahi sis u look take away sossai kika yi kyau kamar ba ke ba hamma ya iya kiwo
  Hhh kai aisha humaira
Wallahi da gaske nake miki fa to shi kenan godiya dubu.

Kin ban sha'awa sis kin yi kysu hamma na son ki kina son sa kuna soyewar ku kamar ba ku ba amma ni da aure a kaina kusan how many years wanda da me sona ne da tuni mun dan tara
  Hmm aisha humaira kenan bari cewa haka wallahi yana sonki tsabar tsantsar miskilanci ne
Menene alamar so ne?
*Kulawa*
Naga kulawa a tare da ke a idan hamma masdoo.
*damuwa*
Naga damuwa a idansa lokacin da baki da lafiya.
*kishi*
Naga kishin ki zallah a tare da shi lokacin bikina.
  Sossai hamma na son ki
 Ki daina kare yayan ki dan Allah ni na san baya sona
 Wallahi baxan yi kaffarq ba hamma yana mugun son ki kuma kema kin san da hakan nagani a idan sa
  Ki daina bin zancan idanuwan nan ki daina sauraran su in ba haka ba zasu yi decieving naki a barki a ruwa.

  Kinga mu canja topic banda lokacin wannan zancan yanzu.


**
Kwance yake a kan gado ya kasa katabus kawai daya kulle idanuwan sa surar matarsa yake gani
 Idanuwanta ke masa yawo a idan sa
 Yadda take tsiwa,murguda baki,masa rashin kunya burge shi yake yi.
  Ya mike ys jingina da bangon gadon nasa ya Allah meke faruwa?
So wata zuciyar ta bashi amsa
 Ya juya da kyar no bani son ta mesa zam dinga tunanin ta haka kawai
  *Ni wacce ita a guna*?
Matar ka,halalin ka,masoyiyarka.
Duk duniya ba wanda zai nuna maka so kamar ta *aisha humaira*
Tana son ka mugun so tun kafin ta san ma'anar so take son ka.

Wayar shi ya dauka ya kunna dan tun safe a kashe take
   Data ya kunna ya leqa watsap family grp nasu ya shiga an tutura hotunan bikin yusuf da amira
  Suka gama budewa gaba daya humaira tayi kyau wani hoto ne ya dau hankalin sa sossai wanda humaira tayi ita kadai ta yi mugun kyau
  Ga killar smile data yi
Shi ma besan sanda yayi murmushi ba a cikin grp din ya dau nuj ta.
   Da niyar zai kirata a waya.

Wanka ya fara yi yaci ado yayi kyau ya sha turarw yadda kasan shi ne ma turaren ya dau tsadaddan takalmin sa ya saka ya dau key da wayar sa ya kulle gidan nasa.

Mota yq shige abunsa ya juya mata kai yayi gaba
 


_kuyi_ _hakuri_ _na shiga busy_ _ne_ _shi yasa kuke ganin sa kadan kadan amma dana samu saukin abunda nake yi zsn kara yawan sa_
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*Aisha humaira*
✨✨✨✨✨✨✨
*Na*
*Khairat up*
*23-24*
*(2017)*

   Cikin nutsuwa yake tukin tamkar bashi da wata damuwa kwata kwata a tattare dashi
  Hankali kwance yake tafiya yana dan murnusawa.

Cikin hour biyu da rabi ya isa inda yake shirin zuwa ya karasa layin su ya parker motar shi cikin yan dakika kadan ya parker motar ya fito abunsa.

Bangaren su ya fara isa ya samu mama kwance kan kujera tana hutawa
 Salamu alaikum
Amin wa'alaikum sallam wa nake ji kamar masdook?
  Mama ni ne
To amma nayi mamaki shekaran jiya fa ka tafi
 Wallahi mama kawai na dan dawo ne
 To sannu da hanya tashi tayi ta dauko masa ruwa me sanyi ta zuba mishi ya kurba
Kaje ksyi wanka tukuna se kazo ka ci abinci ka huta
Ai mama yau zan koma fa

Hba dai kamar ana korar ka tashi kaje kayi yadda nace maka yaushe zan bari ka koma yau tsaka da yamma sossai.
Mikewa yayi yana dan murmusawa.

Da ya gama kimtsawa ya shirya yayi.cikin gida gurin su baffa ya je suna zaune kan tabarba a tsakar gidan suna cin tuwon dawa miyar busasshiyar ku'bewa.

Ya tsuguna ya gaida su dukka suka amsa faram faram
Aa masdook sannu da hanya ka sha hanys ko
Wallahi baffa ya aiki
Alhamdulilahi!to masha Allah
  Baffa dama gun ku nazo
To lafiya dai ko?
Baffa lafiys lou dama akan maganar aisha humaira ne
To bismillah
Baffa ina so cikin sati biyu daza su zo a yi kokari a yi bikin nan ta tare a can ina da bukatar ta q can.

Eh to muma munyi wannan tunanin amma se muka ce mu bari tukuna ta samu makaranta a can garin seta koma .
  Baffa ,abbi duk bazai zama wahala ba a gareni da ita yafi sauki a can in ta samu ai tana garin
  To shi kensn masdook zan yi wa da'ada da iyayen naku magana
To baffa Allah kara girma da arxiki
Amin amin!

**
Tsohuwa me ran karfe kin ci zamanin ki kina kuma cin na wasu!
Ta murmusa kawai.
Kin wani kashingada kin yi wani fresh me sirrin ne tsohuwa.
   Unbula ta masa
Yayi murmushi yana gyara zaman sa a kasan kilishin dakin
Da'ada ya kike ya gdan ?
Lafiya lou masdook ya aikin naga shekaran jiya muka rabu har ka dawo ?
Kawai hutawa nake da yau zan koma amma mama ta hsna wai se gobe ni ku nazo gani dama
  Tayi murmushin manya ta ce masdook lallai ka girma ko dai gun matar ka kazo ?
 Ya sosa keyar sa yana murmushin jindadi
Kai tsohuwar nsn da fassara kike
 Yoh ai abun ne yazo dani da kai zamanin mu daban bar gani na da hurhura a ka ina da sani tun farko
  Uhm lallai ins matar tawa?
Ai wannan ja'irar ban gants ba tunda tace min zata shiga gari gun amira nace ta tambayeka a waya taki ban kuma ganin ta ba ko tayi fushin ne tana dakin inono ko kuma tayi gun matar ismail.
To bara na duba ta.
Dakin inono din yaje suka gaisa rimi rimi ya tambayeta matarsa itama ta fada masa.

Gida ya koma gun mama tana jan carbi a hannun ta zaunawa yayi kan kujera dan ta karasa amma iya kaduwa ta gama ya gama kaduwa .
Tana gamawa ya tsuguno a gabsnta
 Mama kin san inda aisha take?
  Uhm tana kastina man.
 Mama mesa kika bsrta ta tafi
  Da kamal na hadasu ya kamata a ce yanzu sun dawo ma ko me ya tsaida su oho?.
Mama ni ban san fita wallahi
  Yau naji ikon Allah masdook me zan yi to?.
Mutum za a rike shi ne kamar marar yanci?
Mama ba hakq bane ban san fitar ta ne.
 To masdook yi hakuri ba za a kuma ba nayi laifi nayi iko da matar ka na daina.
Allah huci zuciyar ki mama kiyi hakuri ba haka nake nufi ba
Ya fice waje abunsa.







✨✨✨✨✨✨✨
*25-26*

Dakin sa ya shiga ya dauko wayar sa.
  Hello kamal!
Hello hamma an wuni lafiya?.
lafiya lou
     Kun taho ne?
Aa hamma
Se yaushe?
  Wallahi bsn sani ba
Kamar ya?
Aisha din ce taki.hanzartawa nima ita nake jira.
   Bani ita a waya
Tana cikin daka amma bara na kirata sena kira ka.
 Kudin ka ne?
Aa
To kirata ina jin ka.
Cikin dakin ya shiga ya mika matq wayar amsa
  Me?
Ban sani ba
Karba tayi ta sa a kunnen ta
Hello!
  Be tsaya amsa matq ba ya fara magana
""Ki yi maza ki fito ku taho gida ina jiran ki kar ki sake na kuma kiran ku a waya"""
  Zumburo bskin ta tayi cikin masifa.
  Ban ji kin amsa bs ya fada da tsawa tsawa
Ta zabura ta mike
Naji !
Mikqwa kamal.
 Kai kuma ka tabbata kun fito yanzu kun taho
 To hamma yanzu zamu taho.
 Ya kashe wayar.

Kinga me kika jawo mana ko?
Kin san hamma ba kirki gare shi ba yanzu ya ma mutane ihu a waya
 To kayi hakuri mana hamma
Suka yi sallama da amira sannan suka taho gida.

***
A farfajiyar gidan suka same shi gaban ta yw buga dum tsabar fargaba domin kuwa idan shi sun rine sunyi ja dasu.
 Hamma kamal ya yi ciki da mota dan ya parker ta ni kuma kaina na sadda kasa kamar munafuka zan wuce
  Da hannu ya min nuni da na zo
  Jikina na bari na karasa kusa dashi.
 
 Tsugunawa zata yi ya zare mata ido ya mata alamu da ta mike tsaye ya kalleta ta kalle shi
  Humaira!
Na'am hamma dan Allah kayi hakuri wallahi
  Shhhhhhhh!ki min shiru ki min shiru mara kunya kawai uban wa waye yace kiyi waje baki fada min ba haka kike ce min kina sona?
Bayan ban isa ki tambaye ni zaki wani guri ba saboda ni makiyinki ne
  Aa hamma dan Allah kayi hakuri kaji wallahi bansan zaka zo ba kuma ni nayi niyar fita na fadawa dada amma taki bsri na
  Shi ne kiks yi gaban ksn ki
Aa hamma na tambayi mama fa ita tasa hamma kamal ya kaini can katsinan.

Da yamma tayi hankalin ki be baki kiyo gida ba
Shiru ta masa kamar ya mareta haka yayi mata tsawa.
Ta zabura kqmar ta gudu
  Kinyi na farko kin yi na karshe kar ki kuma
To insha Allah bazan kuma ba.
  Anjima ki kawo min shayi da abincin dare ke nake so ki girka min dan *a sanadin ki nazo*
Bambarakwai taji maganar ta kura masa ido
 Kina kallona menene?
Ba komai cikin gida ta koma gun dada.

Wai ina kika je ne?
Katsina naje
Katsina?
Eh me kike ihu kamar baki sani ba
Kin rika aisha
Da na yi me ?
Au tambayata ma kike yi
To matambayi na bata ne?
Mikewa tayi bara na yi wanka nazo na dora masa girkin kar ya samu damar zalintatw kuma
ai gwara ya zane min ke
Dada kenan ko guba ne zan iya sha saboda shi me kums dan ya dakeni ai dadi zanji ma hannun shi a jikina.dada ta kama bakin ta cikin alajabi wannan wane irin so ne humaira kewa masdook.
    *(eternity love)*

 _barka_ _da_ _safiya masoyana_ _ina muku fatan alkhairi_ _da godiya a gareku_ _wajan karfafa min gwiwar cigaba da littafin nan_
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨
*na*
*khairat up*
*19-20*

Nunata tayi da dan yatsa kar ki sake ki min maganar banza marar kunya kawai ban badawa kizo ki kwata kinji.

Waje tayi dauke da jaka rataye a hannun ta mayafin ma ta dan dosana shi a kafada tayi dakin inono

Salamu alykum
Wa'alaykum salam,
Inono zaji je unguwa kuma banda isssan kudin mota kuma zan yi tsaraba kidan rabani man a jakar ki
  Ina zaki haka?
Gun yar'uwata zani je
Katina din zan barki kije a mota ke daya?
Uhm zan iya ai
To badani ba kin fadawa mijinki?
Wai kowa seya ce na fadawa mijina ni banda ma num shi kum...
  Kinga fita min a daki kin ji ko?
Tayi waje tana kumbure kumbure sai gidan su hamma masdook din ta shiga
 
Mama na daka a tsakar kida ta zauna suka gaisa sossai har da tsokanan ta
  Mama zani gidan amira kuma na kira wayar shi bata shiga kuma su dada sun ki yarda na kira shi banda isassan kudin mota nikam.

  Tayi shiru mama ta bita da kallo to ina zuwa dakin ta ta shiga ta dauko wayar ta num kamaludeen ta kira bugu daya biyu ya dauka
   Hello kamal !
Mamana ina wuni
Lafiya lou
Kana ina ne?
Ina bayan layi gidan su zaid
To kazo yanzu ina jiran ka
To mama gani nan zuwa.
Youwa.
 Suna hira suka ji sallamar sa
Msmana gani nan ina labari
  Uhm amshi key dina ka kai min ita gidan amira
  Na shiga three mama kt zani yanzu?
Eh man ko kana da aiki ne?
  Aa mama kawai na gaji ne wallahi kin san fa yadda muka yi zirga zirgar garin nan a kwanakin nan
Toh shi kensn ai se kayi ta hutawa ai
 Yi hakuri mamana bani muje matar hamma amma can zan barki ko ?
Ta dan yamutsa fuska jim kadan tayi magana eh can nake tunanin kwana kawai gobe da yamma  ka dauko ni
  Ya tsaya kallon ta cike da mamaki mamana kina ganin humaira wai ta girma haka
  Dariya ta musu kawai ta ce a dawo lafiya amin.

Suna tafe suna hira haka suka dau hanyar kt .
  Ran ta fes fal ta ma manta bata yi wa dada sallama ba .
 Sede suji a salansa.
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨
*Na*
*khairat up*
*27-28*.

Irin wadda ko bayan rai se anyi maganar soyayyarmu wadda ta fi ta *hilal da ilham*
  *(Khairi nace anya kuwa)*?

Wanka tayo ta saka wata atampa kalar dorawa da dison ja a jiki ta fesa turaren *HUGO BOSS*
Ta daura dankwalin ta irin ture kaga tsiyar nan ga kayan yayi mugun kamata iya damewa dai wannsn skit yayi mata ga rigar kamar kirjinta zai faso ya fito waje  ta shafa lipa gloose tayi kitchen ta dauko kaza dan hamma ma'abocin son gaza ne ta sarrafa ta ga yaji da abincin yayi ta yi masa jellof din talliya dan yana son taliya ta juye a kula sannan tayi blending kayan marmari ta sa suger da kankara ta zuba a jug.

Dakin shi ta nufa tana shiga kamahin turaren *philips lumea* ya bugi hancin ta duniya tana son turaren nan saboda mesa turaren har ranta taji kamshin ya shige ta.

Yana zaune kan gadon shi yaji shigowarta juyowa yayi gareta yana kallon ta ba karamin kyau ta masa ba
  Saukowa kasa yayi ya zauna yana tankwashe kafarsa ,
  Russunawa tayi gefen sa ta ajiye kayan abincin zuba masa tayi ta ajiye masa a gaban sa kamshi ya bugi hancin sa
  Ina fata dai babu yaji a abincin nan ?
Tsuru tsuru tayi da ido
Ya kai loma daya bakin sa yaji yaji ya kalleta ya kurbi ruwa sena hukuntaki dan da gayya kika hambada min yajin nan dan na miki fada amma sena hukunta ki .
 Hamma ka bari kar kaci kaji dan Allah sena maka wani abincin mara yaji .
  Kina tsoron hukuncin ne?
Uhm niba hukuncin nake tsoro ba illar da zai maka nake tsoro dan bani son abunda zai illata lafiyar ka ba.

Idanun sa ya lumshe zarazaran gashin idanun sa suka kwanta kan fuskarsa a ransa godewa Allah da yake yi da ya bawa aisha humaira son sa matuka iya makura yayi dacen mata amma a fili yana bude bakin sa keda wuya ya ce
   Ai raba zafin zamu yi nida ke
Cikin tsurewa ta mike zumbur zata fita dan aisha humaira akwai tsoro.

Hannun ta ya kamo fadawa kan sa tayi ya riko ta zageye da hannun sa zuwa cikinta gaba daya ta rude ta dinga rawar mazari dan fargaba.

Bakin sa ya sa cikin nata ya dinga tsotsa kamar wani lollypop ya dinga mata salo irin na daddadan dan duniyar nan ya kasa tsayawa iya nan kawai seda ya zuge zip din rigarta rigar ta fado kasa tayi maza ta sa hannun ta rufe kirjin ta
   Hamma me haka?
Hukunci ne xan miki dole mu raba yajin tare
 Na shiga uku hamma ka bari dan Allah wallahi na tuba
  Da iya karfin ta hankade shi ta yi maza tayi hanyar kofa cikin taku daya ya cadkota ya hadata da kofar kirjin sa na gogar kirjinta

   Ya sa hancin sa yana shinshinar wuyan ta ya na kissing nata ya hada hannun ta da kofar hawaye ke zuba mata a fuska

Rigar ya maida mata ya zuge mata zip din sama sannan ya bude mata kofar da gudu tayi waje tana haki.

Gurun ya tsuguna ya fadu ragwaf tsabar kasala ya kulle idan sa cikin sa na murda masa besan mesa ya yinhaka ba besan meya rude shi ya aikata mata haka ba
 Yanzu shi krnan zata raina ni
  Kunya yake ji ma shi.

Dakinta ta fada ta kwanta tana kuka me hamma ke nufi jikina ko ni yake so ?

Inko jikina yake so lallai za ayi wadda za ayi jikina yayi lakwas ya hadani da kasala jikina yana kamshin turaren sa na philips humea.

Hawaye sirara suka zubo mata ina ma ace sona yake dana nuna mishi nima son da nake mishi.

Haka bacci ya dauke ta bata farka ba sai asuba tayi sallah sannan tayi wanka ta koma bacci abunta amma baccin yaki zuwa kawai hamma masdook take hangowa yana rikita mata kwanya gaba daya ta kasa manta jiya balle abun jiyan
Tsaki tayi shi yafi a kirga ta juya kuwa iya juyawa kan gadon ta so ko wahala
Mtsw mutum yayi wa mutum katutu a zuciyar sa ya hana shi sakat ys hana shi yin komai sai aikin tunanin mutum overoll ma mutumin da ba son ka yake ba .
Allah ka yaye min amin.

Masdook dama yau zai koma bakin aikin sa bayan nan kuma za ayi yan gyare gyare a gidan kamin zuwan matar sa.

Gaba daya ta gama rikita shi ya gama kamuwa shi kqm gwara a kawo masa matar sa shi ba walliyi bane yasan bazai sha wuya ba dan kuwa matar shi son shi take babu wani limit why not .......
  Wani murmushi yayi wanda ni kaina ban san me hamma yake nufi ba .







29-30

   Wai ni ibrahim tunda mutanen nan suka tfi da yarinyar nan baka taba zuwa kaga halin da take ciki ba ko me take bukata baka tsoron hakkin Allah ya kamakq yarinyar nan diyar ka ce halilinka jininka amma kayi irin shariyar gareta na tabbata ko za a kashe ta a hanya ta ganka kaima ka ganta bazaka ce ga yarka ba balle tace maka baba ko kai ka gane jinin ka ce kai ba abun kunya bane a gareka ?
   Ya kai lomar tuwon bakin sa  ya na juyowa hajiya kenan ai ni banda abun cewa ban san naje su kuma min kallon silar diyarsu a fada min magana ni kaina fa uba ne kuma ina da buri kan yarinyar ammq kin san na kasance mutum mara son hayqniya tun filazal.
  Ni kaina ina son na ganta
Na ga yadda ta koma
Na mata gata irin ta uba na nuna mata zallar kulawa
Sede kash Allah be so hakan ba amma ban fidda rabo ba zata neme ni
 Kai ta gyada masa har kana tunanin zata neme ka?
  Hajiya yar aisha ce fa aisha kuma zuciyatq ce ni kuma yar aisha yata ce jinina ke yawo a jikinta ta ko ina nata tunda ina raye zatq neme ni ko da bayan raina ne amma ni nasan zata nemi baban ta ai da uba ake ado.

   Allah sa hakan amma ibrahim diyarka karka manta a ina ta taso
 Ban manta ba kuma bana ganin laifin su sam sam domin nina jawo nine sila da abunda ya faru be faru ba da hakan bata kasance ba amma ba wanda ya wucewa kaddarar sa babu shi a duniya.
  To Allah karq mana imani amin.


**
Da wani isa yana batsewa ya shiga dakin dada tana shan koko aisha humaira kuma na shan tea da biskit taji zuwan shi ksnta a kasa ta gaida shi bayan ya gaida dada
  Zuba min tea mana!
Hada masa tayi ta ajiye masa a gefe fuskar nan murtuk tsabar fushi ita haushib sa take ji gaba dayan sa
  Wurin ta ta koma ta cigabada karyawa abunta.

Dada na gamawa ta mike zan wuce
Ai se ki bari na gama na raka ki ko ?
Na hutashe ki amma nikam har yau da kwarina
Dada wai ina zaki haka?
Wallahi dan nan gun aminiyata zan je a can makota
  Yyi dariya wai Allah dada har wata aminiya gsre ki
 Ta masa unbola amsa na baka nake ne
Tuba nake a dawo lafiya kiyi yawo kila kashin naki ya sake kullum zama gu daya kamar an dasa ki
  Kai kan akq gwada nafi tsohuwar ka kwarri nifa tsohuwar jini ce ba ta zamani ba
   Yayi dariya sosai sekin dawo dada Allah kiyeye hanya ki tafi mata da tsaraba
   Ficewa tayi abunta ita kam.
Dakin yayi tsit kuma na yan lokuta
Tana gamawa ta mike zata koma daki
Zauna .ya fada ta koma ta zauna tana kumbure kumbure
 Ki kasance cikin shiri ko wanne lokaci daga yanzu za a iya cewa za ayi bikin mu .
Ta dan kalle shi ta kyabe fuska
 Ni in fadama wani abu hamma?
Ina jinki yq fada yana dana wayar sa
  Ni dan Allsh ka sauwaka min wallahi Allah na hakuri ni bani son ka ka sauwaka min na auri me sona bana son wanda baya sona abunda na fada maka a baya duk yarinta ce yanzu na daina ba dole ka soni ba kaji nayi quiting.
  Wannan maganganun da take be dago ya kalleta bama yace kin gama?
Eh
To bazan sake ki ba kiyi duk wadda zakiyi kinji ko tunda kika ce *kina sona*to se mun zauna tare ai dama na fada miki zaki yi dana sanin aurena ba kin ce *ke ni kike so ba ?* to muje zuwa muyi *son* tsabar tsaurin ido irin naki ni zaki cema kina so ki min wannsn bomb din a dangi ai kinga gwara na hukunta ki ko ?
  Hawaye ya zubo mata Allah ya sani tsakani da Allah da zuciya dayq nake sonka amma kai bani kake so ba sha'awata kake yi tayq zan zauna da kai.
   Dariya yayi kasa kasa humaira kenan yo ai na cutu ince ina sonki ke kan ki kinma kan ki karya ko jikin ki nake so ai nawa ne tunda na biys sannsn akq bani
me a ciki abun fa trade by barta ne kina son masdook na yarda na aureki to masdook kuma jikin humaira yake so kuma nq shi ne ba shi kenan ba anyi one one ?
  Tq mike Allah ya kiyaye wallahi bazaka samu ba .
     Haka nake son mace da confidence kin burge ni jiki ai kamar na gama samu ne kawai ki kwantar da hankalin ki zan shayar dake ruwan love yq fada yana mata dariyar mugunta
   Zata yi dakiyace by the way lips dinki akwai dadi fa
da gudu ta koms daki tasa key ta fada gado tana kuka na shiga uku nikam wayyo Allah na najawa kaina.
Insha Allsh bazaks samu nasara ba ksn mugun nufinka!

Tana shiga ya dinga dariys matsoraciya kawai zaki yi mamakina in kika ga new masdook mijin aisha humaira

_sabahulkhair_ _♡ u oll fans na aisha humaira_
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨
*31-32*.
*na khairat up*
Cikin shadda hilton milk colour ya fesa turaren sa na philips humea ya sa takalminsa dan paris ya daura agogo ya taje gashin kan sa ya shafa masa mai ya yi waje dakin msma ya nufa suka gaisa yace mata zai tafi shi kam
  Tun yau ?
Uhm
To Allah kiyaye hanya
Kaje gun amira kuwa?
Ya sosa keyar sa mama zan biya in zan wuce a min ahuwa ina kunya ne ni babban wa
Kai baba yaushe zaka rage wannan kunyar kamar mace ya kamata kaje kam ta ji dadi itama ai
 Insha Allah mama zani je ni anjima kafin na wuce
Allah ya bada iko
Amin.

**
Baffa na gama shiryawa zan koma gun aikina
To to Allah ya taimaka ya bada sa'a ya kiyaye ka daga sharrin masharata
Amin baffa
Abbi zan wuce
Allah kiyaye hanya
  Sanda yaje gun dada suyi sallama tana sallah yayi murmushi tsohuwar nan akwai ta da ibada.
  Dakin humaira direct ya shiga tana charting a waya
Sarai taga shigowar shi kuma taji muryarsa kuma over oll taji a jikin ta
  Ta gyara zaman ta tana cigaba da abunda take yi.
 Ya zauna bakin gadon yana mata wani kallo
Wanda se da ta tsargu ga'ba daya ta gaji da yadda yake mata kallon up and down ko ina a jikin ta yake bi da kallo
  Ta ajiye wayar a gefe me kake kallona haka ban san kallo fa
 Da wane idon kika ga ina kallon ki in ba kema kallona kike yi ba ?
Uhm Allah ya sauwake mezan kalla a nan?
Kafarta ya jawo ta zamo kusa dashi abunda kika gsni kika ce kina sona kinga handsome me kyau
Hararsa tayi hade da masa tsaki bata yi aune ba ya matse bakin ta da yatsunsa guda biyu tayi kokarin kwacewa ya rike daya hannun nata da daya hannun ya murda shi baya hawaye suka zubo mata tsabar azaba.
  Kinga kuwa yadda kika yi kyau kuwa?
Ya mata hoto da wayar hannun sa yana dariya kullum sena kalla nayi dariya na hango munin ki.
  Ya sake mata bakin ta yana murmuahi irin murmushin muguntan nan
 Nasan ni kike so bazaki kula kowa ba na sanki da hakan ko ina zan miki wannan shaidar amma duk da haka ki kula min da aurena dake ksn ki bands shigar banza banda yawon banza num shi yasa a wayarta ya kira layin sa
Good na wuce ni sena dawo daukar amaryata ke kenan ki kasance cikin shiri.
  Yayi mata sumba me karfi me tsayi
Sannsn ya wuce abunsa.
Kusan mintin shi uku a soron da zai sada shi da waje yana maida numfashi daga bisani kuma ya shiga motar sa ya koma gun aikin sa.






*33-34*

*_bayan sati uku_*

Satin bikin ya matso lokacin kuwa aisha ta samu add a makarantar bayero ta samu medicine a buk se murna sossea ta kamata

Ana saura kwana biyu ayi kamu mutumin ya sauka a garin dikko da lefen shi ya taho nas da ni'imatullahi suka shiga da akwatuna dakin dada akwatinta guda shidda na sa rana guda shidda na lefe ba karanin kaduwa tayi ba da ta ji irin kayqn da masdook ya mata ba sossai tayi mamaki anya kuwa hamma masdook?
Hmm Allah masani
Aka dinga yarinya tayi goshi waye ya mutu waye ya tashi
  A cikin family house dinsu aka yi taron kamu inda mutane suka dinga zuwa autar dada yar gatan dada masoyiyar dada.

Ta sha shiga ta alfarma ta zauna a kasa inda aka mata jere irin na kumbu na yar gatar amarya tace bata son wayanan kyalkyale kyalkyalan na biki.

Ta zauna fuskarta lulube da mayafi me ruwan gwal ta sha adon gwalagwalai.
Masu kamu suka kama amarya inda tasha turaren intemately becham.guri ya dau kamshi.

Washe gari aka yi wuni dama wayarta a kashe take dan bata son damuwa

Shi kuma se kiranta yake yi a waya amma a kashe yake ya kira amira ina humaira ?
Hamma tana cikin mutane
To me kike nufi?
Tayi masa shiru
Ina magana?
Hamma zuwa zan yi na dauko ta na bata waya kasan cewa bazan iya cewa tazo kana kira ba inonono ma magana zata yi anjima zan kawo ma ita amma yanzu kam..
Wallahi ko ki bata ko na shigo gidan
 Hamma ni mezan ce kuma?
Ubanki !
Ta zumburo baki ta shagwabe fuska hamma bara na bata wayar
  Ta kutsa cikin mutane ta mika mata wayar
 Waye?
 Mijinki!

Kina kallo ina cikin mutane taya zan amsa wayar kuma?
Ke kika sani ni bazan iya ba kun sani a tsakiya.

Hamma kaji ai da kyau ta kashe wayar mijinki ya fiya kalula da fi'ili ni kam ku karata harda zagina fa yayi .
Tayi mata dariya kice yau kin samu rabonki


Da daddare akayi mothers eve.
Washe gari akq kuma daura auren masdook da humaira.
 Yan gaban goshin dada bakin tsohuwar yaki ruhuwa dan dadi

Yan matan na zaune a tsakiyar gadon humaira suna ta tsokanarta angwayen suka shigo dakin suna hira a tsakanin su shi ko uban gayyar bakin sa gum yaki tankawq bare ya tofa amma ya bita da kallo shadda ce a jikin ta doguwar riga yasha aikin gana ta yi kyau ta yi daurin nan me hawa hawa gashinta daga baya ya fito
  Amira ta rangada mata kwalliya irin ta zamanin nan tayi mugun kyau mayafinta me tsada ta ajiye shi a gefen ta.
   Kamal yace amarya amarya for the second tym an daura auren ki da mijinki masoyin ki wanda kike so har a zuciya buri ya cika.
Aka sa dariya
Wallahi ban taba ganin me son mutum ba irin aisha humaira yadda take son shi kamar yadda laila take son majnun.
  Gaskiya kam Allah ne ya hada su
Ita dai tsna jinsu bata ce komai ba shima yana jinsu be ce komai ba illa kallon ta da yake yi kawai.

Suka gaba tsokanarta
Yace to nagode fa kun yi hirar da yawa kun dami matata
  Nas yace ohhhh *matarka*
Suka yi dariya gba daya hamma yusuf yace muje mu waje kafin yace mana *get out*
  (Hhhhhhhhhh)gaba dayan su suka yi

Dayan bayan daya suka dinga fita daga dakin aka barsu su kadai
   Inono ta leqo masdook zamsn me kake a ciki?
 Ganawa zan yi da matata kinsan an dade ba a hadu ba

Ta kama haba lallai masdook ka rika ta koma waje .
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨35-36✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨na khairat up✨

Harara ta sakar masa hade da mikewa zata fita ya yi maza ya kulle kofar ya hankadata kan gadon dake dakin
 Ta juyo idanunta masu kalar bacci ta zuba masa
 Yasa hannun shi a kirjinsa yana dan shafawa wow!ina son kallon nan
Ta juya ta gyara zaman ta tana me sirfa masa harare harare kala kala .

Ya kwanto kan cinyarta ya dan rankwafo da fuskarta kan nasa ya soma sumbatar bakin ta kamar wani zaki daga kwancen ya masa tsauri ya mike ya koma kqnta yqna aika matq da sakwannin love me wuyar dauka a gareta .
  Turesa take ammq a banzq kamar dada angiza shi take yi cikin kuka tace haba hamma me hakq wai da mutane fa a gidan ka manta taron biki ake yi wannsn ai rashin kunyq ce ba dabi'ar mu bace ka tashi ka tafi dan Allah.
Shhhh ya dora yatsan sa a bkin ta ki min shiru saina gama abunda nake yi tukuna zan tafi kome za a ce a ce a shirye nake.
 Na shiga uku wai me haka ka manta wacece ni a gunka?
Matata ce
 Hamma ka manta kace niban isa komai a gunka ba dan me kuma yanzu zaka rude a nan?
 
  Ya cikata yana kallon ta da sexy eyes na shi da suka koma ja dan jaraba tsoroma yake bata ita kam
   Jikinta sai rawa yake yi ya kalleta hade da nuna mata dan yatsa 👉🏻 look humaira kar ki yaudari kan ki ki dauka cewa son ki nake babu shi a dictionary dina ba sonki nake ba
  Ya ja hannun shi kan jikinta yana zagayawa dashi jikin ki shi nake so ke kike sona masdook yake son jikin ki so kin sameni nima dole in sami abunda nake so.

Siraran hawaye suka zubo mata masu zafi da daci a zuciya ta kuma kallon sa ta mike da kysr dan jikin ta ya gama mutuwa da kalaman hamma masdook
  Hamma tabbas ka gama dani ka tuna yadda nake sonka haka zan iya daina sonka kuma na ji duniya ba wnda na tsana irin ka
*Get out daga dakina ta fada cikin tsawa so ba haukq bane na daina son naka mezan da kai marar imani mugu wanda besan darajar so ba ta juya a fusace kai wa ma zaka iya so ? Babu yadda ka min saika rasa me sonka zaka yi kuka a kan so*

Mari ya dauketa dasu kwarara guda biyu wanda seda taji kunnen ta ya dauke ji na yan sakwanni ta tsuguna a gurin tasa masa kuka .
 Tsugunawa yayi a kusa da ita yana devlish murmushi
*welcome to hell humaira*
  _Welcome_ _ina miki marhaba da zuwa gidana gidan da bazaji ji dadin sa ba gidan da kullum sekin zagi ksnki dalilin zuwan shi se kin yi danq sanin aurena ko sanina zaki san cewa ni din bana wasa bane stupid girl_

Nima na maka alkawari bazan hanaka komai ba a kaina amma zaka yi repenting lokacin ni kuma zan nuna maka ainihin aisha humaira.

_I like promises yadda kika rabani da love of my heart haka kema bazaki ji dadin love dinki ba ill make sure hakan ta kasance_

Matukar son da nake maka na tsakani da Allah ne ill win over you ka bar ganin sonka we ll be my weekness ko kadan it will be my strength.

Kai ya gyada yana dariya shi kenan ai let the circle start caiculating love angle ya koma war angle
  A gunka love is bad a guna love is good kayi da yar halak wallahi masdook muhammad dikko seka soni so na hauka sona har abada so na ba mantawa so wanda kai da grate masdook seka yi *kukan so*i promise you that

_Well muje zuwa i ve d trupm card_
_And i ve the king in my hand_

Hannun shi yasa ya jawota jikinsa ya matse ta da hannun sa rike da kugunta jikin su na gogar na juna we shall see ya sa glass din sa a ido ya hankadata ta fada kasa
  Tun a nan kin farq faduwa? Nan gaba ya kenan ?
_hmm ko wa seda ya fadi yq tashi so falling and raising in love is normal yau nina fadi gobe kai zaka fadi principles da rules na love kenan ai_
So mr.masdook dikko get ready to fall in love
*Never*

 *😀you most dole ne ma ai u most fall in love*
Ya juya ya bude kofar ya fita abunsa
Tq baje a gun tana kuka kukan tausayawq kan ta daga bisani ta mike ta share hawayen ta bazan taba bari yayi winning ba sena ci galaba a kansa sena nuna masa cewa true love always wins
True lovers are always blessed by Allah.
Son da nake ma hamma na tsakani da Allah ne na har a zuciyq ne son da nake maka is limitless komai zanyi a kanka
Son da nake maka karfina ne ba ragwantq ba zan baka mamaki.



_is love month khairi na mika gaisuwa gareku masoyan aisha humaira weekend mubarak ❤💄😘

Ina magoya bayan humaira?😜
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨
37-38
*na* 
*khairat up*

_happy birthday my dear sisi aisha muhammad lame its ur day sweethart Allah's khair and nur be with u Allah kawo bikin ki mu dance miji nagari fata amin_

_Wannan page din na kowacce aisha humaira ne_


   Wanka tayi ta kwanta tsabar gajiya ga takaicin da masdook ya guma mata ga shi kaunar shi ya mata katutu a zuciya ya hanata sakat ta rasa dalili a kan sa duk wani tsiwa da wulakanci nata bacewa yake yi bat kamar ba ita ba sometimes ma tana zargin kanta anya ita ce kuwa *aisha humaira*?
Mtsw
  Bacci be wani dade ba yayi awon gaba da ita ya dauketa dan ta gajin daman.

***
Dakinsa ya koma ya shiga toilet ya sakarwa kansa 🚿 shower yayi wanka dake ma ma'abocin ruwan sanyi ne shi
In dai yayi wanka da ruwan zafi se 'kuraje sun fito masa a jiki .

Siglet da short ya saka ya kwanta kan gadon sa gaba daya artabun sa da humaira yake tunawa wai wannsn wacce iriyar yarinya ce me kaifin kai da tsaurin ido ni ta kalla ta fadawa waddanan maganganun kuma i just left her she's daring gaskiya kam yarinyar
Wasan namu zeyi kyau kam amma ya zama dole na koya mata hankali i wont let her win
Mtsw kawai a hada mutun da jaraba yoh ai humaira jaraba ce dan ta maidani jarababbeb karfi da yaji na zama mayan mata da kunnena shiru hayyan
 Mtsw alakakai.


Wanka ta sake aka yi wuni aka gama da daddare kuwa dakin inono ta kwanta dan ta gaji da yawa a dakin dada yan biki ba barinta zasu yi ba ta huta kila ma wannan mr.arrogant din yazo dan abunda zata dibga kiransa kenan mr.arrogant dan shi ne he deserves the name.


Bata wani jima ba bacci yayi gaba da ita a dakin.

  Inono ta shigo ajiye kaya tayi a kan gado ta ga mutum ta ksma salati au kina nsn ana ta neman ki a can ?
 Inono wallahi sossai na gaji shi yasa na yo nan
 Dan Allah karki fada musu ina dakin.
  Inono bakin kofa take a tsaye ta ce *mindili*
(Tazo kenan)
Da kyar ta karsa gunta
 Jikinta ta taba taji garau
 Dariya tayi kai inono lahiyata kalau wallahi kar ki damu kawai gajiya ce bsn san damu
To.

   ***
   Da safe tun asuba data tashi bata koma baccin ba
Wanka tayi da ruwan zafi sossai sannan ta koma ta kwanta cikin doguwar riga slik pink gaba daya ta kwanta jikin ta luf

Karfe goma daidai ta fito tsakar gida ta gaida ysn tsaksr gidan dan ko gidsn ya ragu da mutane da yawa kuwa dan an ragu tunda an daura auren jikinta duk ciwo yake a corridon dada mi'ka ta kamata

Daga sama taji ana mata magana gwara kiyi ladab na hutar dake kin gaji da yawa tunda kinsan masana sun ce idan mace tana mi'ka tana da bukatar namiji a kusa da ita kizo kawai tunda ke da mijinki a kusa

Hararar sa tayi sannsn tayi tsaki Allah sauwake kai din me
Tayi ciki da sauri
Dariya ta bashi sossai.
Cikin gidan ya bita tana kwance jikin dada
  Nesa dasu ya zsuna ki daga mana dada ksr ki karya ta dan ta tsufa bamu gaji da ita bafa
Harar dai shi ta kuma masa dan ta lura ya maidata abun wasar sa.

Kosai da kunu ta ke ci ta hada da kunun ta har ta gyatse.
 
Tea ya sha da kwai soyayye da bread
Dada dake fa zamu tafi
Allah sauwaka !
In biki barni agidan mijina yadda aka kawoni haka za a dau gawata ehe
Suka yi dariya gaba dayansu
 Fadimatu dake gefe tace dada kyale su ina zaki bisu su kashe miki ragowar idanuwan ki da soyayya ta zamani
Unbola ta mata ungo nan wane soyayya zaku yi ku kam ai soyayya se a zamanin mu ku me kuke yi bsnda shirme.

Hah 😱 dada kina nufin ku kuka iya so?
Fadi ki kara hajiya ku ai sababbin shiga ne me kuka sani?

Mu q lokacin mu mazajen mu ji suke damu muna mutuntq juna ke se ayi aure baku san juna ba se an kqi ki ku ga juna kuma ku zauna lafiya ko yaji bama yi balle aji kan mu
.ku fa abu kadan ayi yaji a koma gida saboda tsiya ina soyyar da bayan aure se fada da hayaniya ba zaman lafiya
Ai abun kunya ne banda yaudara da karyq da fada ba abunda kuka sani.

Ho su dada an tuno da za a sauke mana wahayin soyayya
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
Aisha humaira
✨✨✨✨✨✨✨
*na*
*khairat up*
*39-40*

Kai dada kin zama love guru
Me kuma wani lac gura
Aka kwashe da dariya gaba daya dada ban iyawa da caftar ki yanzu cikina yayi ciwo .
Ke in kin gama ki shirya yau zamu wuce ayyuka sun mun yawq ana ta kirana a can gun aikin

Kamar ya ku wuce masdook ai se anjima an zo se a kai maka ita da kai zata tafi da

Dada kin san ban san wannan abun kawai zan tafi da ita daga baya kwa zo kuga gidan amma yau kam
Yau naji dan banzan yaro an taba haka?
Dada dan Allah kar muyi haka dake ki barni na wuce da ita in kin min haka ai se aji kanmu  a mana dariya dada.

To me kake nufi yanzu?
Ki bari ta kimtsa mu wuce kawai daga nan se kano zan yi report gun aiki

Masdook gaskiya
Dan Allah dada kinji dadata ki yi hakuri na miki alkawari da kaina zan dawo na tafi da ke da mama da inono da sauran yan matan

Hmm amma banso haka ba yanzu ku biyu kawai zaku tafi?
Eh dada
Aa kuje da fadima.
Dada in naje da fadima wa zai dawo da ita yau dan ni kam aiki ya min yawq kamin na samu hutu se na jima kuma ita ba zama zata yi ta yi ba har sena dawo da ita.

To ai shi kenan Allah ya sa hakan shi ne daidai
Amin.
Ki shirya yanzu fa kar na leqo kiran ki
Uhn kawai ta fada amma badan taso ba.

**
Zaune suke gaban baffa da su abbi suna musu nasiha
Kai masdook ga humaira nan amana ce a gurin ka yadda take amana a gurin mu gashi yau mun baka amanar mu ka cigaba da rikewa in ka cuce ta mu ka cuta kome ka mata kamar damu kake wallahi masdook kar ka bari inji wani mugun ji a zaman ku
 Insha Allah baffa baza a samu matsala ba.
Ke kuma masdook mijinki ne ,abokin ki ne,kuma ya zame miki tamkar uwa da uba ysnzu ki masa biyayya iya iyawar ki in yace yi ki yi bari ki bari banda rashin kunya humaira ki zamto mace tagari wadda za a ke kwatance da ita ki.kasance  me bin umarnin mijinki seki ga kun zauna lafiya.

Sannan farkon abunda zaku lura ku kula dshi a zamsn auren ku shi ne *hakuri* hakuri shi ne farkon abun luran ku in baku yi hakuri da juna ba akwai matsala ko wanne gidan aure da haka yake tafe wannan *hakurin* shi zama na aure zama ne na zo mu zauna zo mu saba ,zama ne na amana da yarda to fa ku rike wannan amanar ku yarda da juna
Humaira kar a kawo min karar ki ksima masdook kar a kawo min karar ka
Insha Allah abbi zamu kiyaye mungode
To kuje ku Allah ya kiyaye hanys ya bada zaman lafiys da zuri'a d'ayyaba.
Amin suka amsa kasa kasa.

***
Motar shiru kake ji tsakanin mutanen biyu tamkar ma ba kowa a cikin motar
Gefen ta kswai take kallon hanya shi kuma gogan yana ta satar kallon ta yadda yaga tayi wani fayau tayi kyau kamar ba ita ba
Kawai ji yayi wani feeling na tashin masa ina ma ace ina gida ne ina ma zan iya nuna miki yadda nake da tsananin bukatar ki
Ina ma ina son ki da komai yazo msna da sauki sede kash wannan zuciyar tasa ni cikin damuwa.

Ina ma hamma masdook ze gane irin son da nake mishi nima ya soni mu zauna lafiys ksmar kowa ina ma hamma masdook zai canja ra'ayinsa a kaina da bamu fi haka  ba zuciysta baki min adalci bs kina son wanda baya sonki baya kaunar ki burinshi ya bakan ta miki ina ma ace zan iya cire wannsn zuciyar na cire son masdook daga cikin ta kawai hawaye ya zubo mata tasa hannun ta ta share
Baki fara kuka ba mrs.masdook
Hmm kar kayi tunanin na karaya ne ina kukan bakin cikin rashin yadda zan cire ka daga raina na yarda kai a bola kamar wani datti dan ka zamo dauda me illata takurawa mutum a guna.

Ohh mrs.masdook ai kisani ni kadai masdook nike da ikon zama sanadin zubar kwallar ki ni kadai na isa nayi hurting dinki ba wani ba ke kan ki baki da ikon hurting ksn ki sede ni ya nuna kansa ni masdook muhammad nike da wannsn ikon na takurawa rayuwar *aisha humaira*
Ki dinga tunawa da wannan duk sanda kike bukatsr yin kuka ki tuns cewa masdook ne sila.

Mr.arrogant ko kadan ban jin haushin ka illa haushin kaina dana kasa yakice kadaga rayuwata na watsa ka daga cikin rayuwata
Na rasa ina zan sa ka na kasa tantance me ya kamata na kira ka dashi
Masoyina ko makikina
I hate u ko i love u
Wallahi hamma masdook i just dispite you honestly i dispite you duk sanda na tuna da kalamanka i feel disgust

K then get ready to be dispite always my slave

Kallo ta bishi dashi kawai shi kuma ya cigaba da tukin sa yana wani taunar cingum kamar wata mace .

(Tafiyar da nisa )

********      *******

Kaji me na jiyo kuwa?
Aa hajiya
Auren diyar ka ba tare da sanin ka ba anya ana ma adalci kuwa?
Hmm hajiya nima naji wannan abun amma yazan yi ?
Yazaka yi yarka tilo a duniya kace min ya zaka yi
To hajiya ki fada min ya zanyi me zanyi a lokacin da diyata bata san ni ba bata taba tuna ni ba bata taba yin tunanin dawowa ko zuwa gareni ba

Innalilahi wa'inna illahir raju'un
Dole nayi kuka dan wannan abun takaici ne a gareni ban ji dadin wannan al'amarin ba sam sam ina mugun bakin cikin shigowar wannan matsr cikin dangin mu ina wannsn takaicin Allah ya isa gashi ta zamo mana sila bani da ikon ganin jikata baka da ikon ganin diyarka.
 Hajiya se addu'a
Ka min alkawari koda bayan raina ne ina nemn alfarma ka kawo min yarinyar nsn taga koda gawata ne hawaye suka zubo mata
Subahanalahi hajiya kiyi hakuri dan Allah insha Allah zanje ni can garin zan kawo miki jikar ki ki gsnta amma insha Allah hajiya zaki ga jikar ki

To nagode maka nagode.


*****

Wajan la'asar suka shiga kano ya yi dasu sultan road inda gidan sa yake kawai kallon titi take yi.

Haka suka karasa gida yana parking ys fice kawai tana ganin hska ita ma ta fito ys hude but ya sauko da akwatin ta wanda ya rage ba a kawo mata ba
 Ki dauka ki shigo dashi
Kallon akwatin tayi yadda yake da uban nauyi da girma ta kalli hannun ta kai hamma masdook ko mugu akwatin ma bazai iya taimska min ba har ya shige ciki abinsa ya bsrta gaskiya bsn iya daukar wannsn akwatin harga Allah.

Waje takoma ko zata ga ysro da kysr ta samu wani dan saurayi tace ys taimaka mata haka ko aka yi ya shigar mata dashi palo ta ce masa ta gode ta bashi alheri yace yagode.

Masdook na kallon su ta saman bene kawai ya gyada kan sa .

Nima kairi na gyda kai ina cewa zaka zo hannu ne masdook au me.arrogant
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
aisha humaira
✨✨✨✨✨✨✨
*Na*
*Khairat up*
*41-42*

Kan kujera ta zauna tana kawai tana bin gidan da kallo tabbas yayi mata kyau gidan da dakuna guda biyu a kasa da kitchen da kuma toilet a kasan benen.

 Mikewa tayi zumbur dan ta fi son dakin sama dama hawa saman tayi ta dinga kallon shi dakuna samsn guda biyar ne ta dinga leqawa har ta bude wani dakin kamshi ya doki hancin ta
  Leqawa tayi ba kowa amma taji karar ruwa kamar ana wanka
Wayat shi na neman agaji tayi kasadar dauka
 Sunan taga an rubuta
*zainab*

Haka kawai ta dauki wayar ta dau kiran
Hello masdook dan Allah kar ka kashe wayar kaji
Uhm
Kawai ta fada
Masdook ina son ganin ka dan Allah meet me ina son muyi magana nida kai
Wai ke mayya ce ko me na rabaki da mijina kinki ji kp to wallahi zan hada ki da 'yan'sanda su rabaku mayya kawai
Ke kuma wacece?
Matar sa.

Tsaki tayi gaki nan mayyar kin shiga tsakanina da masoyina kin kanainaye baya son ki dole ne

Haushi ys cika aisha ta kashe wayar ta goge call din ta sa num a blacklist
Komawa dakin tayi yayi daidai da fitowar shi daga toilet din

Rigar wanka ce a jikin sa ya na tsane gashin kan sa ya ganta dakinsa bakin shi ya bude
Dawayo da dabara ta ajiye wayar kan gadon
Ke me kike min a daki?
Ina da ikon shigowa ta fada tana harar sa
Kallon ta ya tsaya yi kawai
Ban baki izinin shigowa ba ai ni
Ni na bawa kaina
Kinga a gajiye nske bana son takura da damu zan kwanta na huta ban san damuwa.

 Ni ka zo ka sama min abunda zan ci yunwa nake ji ta na murguda masa baki

Ki nemi bawan ki
 Ya fada yana jan bargo ya kwanta ksn gadon bargon ta janye daga jikin sa wallahi Allah bazaka kwanta ba seka bani abunda zan ci.tukuna zaka kwanta

Ba inda zanje baki isa ba
Ok haka kace ko ?
Eh na fada
Wayar sa ta dauka ta kira num abbi

Salamu alaikum abbi an wuni lfy
Lafiya lou kun isa lafiya
Wallahi alhamdulilahi
Abbi dama hamma ne
Ta fada tans kallon sa
Masdook me ysyi miki?
Dama wai nace ya.....kwace wayar yayi ya sa hannun sa ya kulle ke bski da tunani dama
Kafadarta ta dage masa alamar i don't care.

Hello ! Abbi ina wuni
Lafiya lou
Meya faru ?
Abbi ba komai shakiyancin ta ne kawai.
Ksi aisha bazsta girma ba.
Se anjima.

Kar ki kuma daukar min waya
Ka kawo min abinci yunwa nake ji.

Key ya dauka fice a fusace yana bala'i a ransa

Wanka tayi ta sake kaya kafin ya dawo ta shirya cikin atampa skirt da riga fitet ta daura dankwali simple ta dauko turare ta fesa

A falo ta koma ta zauna tana jiran sa bata jima da zama ba ya shigo gidsn ds take away ajiye mata yayi a kan center table ya wuce dakin sa.

Dariya ta kyalkyale da dariya kasa kasa yanzu zan fara uzzurawa rayuwarka
Bakin dakin sa ta koma ta kwankwasa yana ji ya dora pillow kan kunnen sa shigewa tayi kawai direct abunta.

Yana daga kwance ta masa tsaye a ka
Me kuma?
Icecream nake so
Icecream?
Eh icecream!
Bazan kuma fita ba
Ai kana sane kk siyowa kasan ina so saboda haka sai ka koma ka siyo min icecream din
In naki fa?
Ta nuna masa wayarta alhamdulilahi ina da num abbi ill just dail d num
Ya mike a fusace ya nunata da dan yatsa ki...
Ta ce ooo dont even start(karma kafara)
Kawai ka je ka kawo min mu zauna lfy.

Wallahi zan dau action akan ki
Ni kuma zan dau direct action akan ka

Hankadata yayi kan gadon ya fuce daga dakin dariya sossea ta kauce da shi tana masa dariyar mugunta zaka sani ai.


Icecream ya siyo roba biyu ys kawo mata tana ganin sa ta amsa tayi waje sannan tace wallahi an yi 1-0
Biyota yayi tayi waje da gudu tana dariya
Kwantawa yayi yace women are *(emotional blackmailers)*
Amma zaki san anyi 1-0 sanda zai koma uncountable zeros dazan baki.
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
Aisha humaira
✨✨✨✨✨✨✨
*na*
*khairat up*
*43-44*

Da wuri ya tashi ya shirya dan zuwa gun aikin sa ya gama shirin sa cikin kanun kaya
Ya fesa turare ya daura agogon sa sannan ya dau key da jakar sa ya fita daga dakin.

A dinning ya tsaya ya saboda saurin da yake ya bude cornflask ya zuba a bakin sa ya sa madara spoon daya da ruwa ya tauna sauri sauri

Dariya yaji ana masa daga baya juyowa yayi yana kallon ta
Sleeping dress ne ajikin ta nylon blue light wayaga gauro mutum da matarsa amma kamar bashi da mata kawai kayi ladab a maka komai irin name iyali ka tsaya girman head 😏

Ni a principle dina ban san na bawa mace hakuri ko na mata godiya ba to ke a suwa ban iya roka ba sede na kwata

Ta zauna kan kujera tana kallon sa ta rike haba ta ce ah! Da gaske ? Ai ban san cewa haka kake da principles ba amma nagode daka sanar min sena zama addicted ko ?

Kamar ya kwade ta haka yaji ga takaici ya kama shi gaba daya ya rasa meze mata jakar sa ya dauka ya kara gaba har yana tuntube ma
Kaje a hankali fa ni bazan iya daukar kato ba
Juyowa yayi ya harareta ya na mata kallon zaki sani !

***

Sun dade suna waya ita da amira;da fadima da rabia suna confrence call
Amarya ya garin?
Lafiya lou
Ya first night din?
Kiyi aure ki sani kema
Au Allah abin gori ne ns miji?
To ai miji ba karya bane
In kinji haushi kiyi auren kema
To aisha humaira tsiwa matar hamma miskili.
  Ke rashin kirkin ki ya tsaya a tsakanin mu banda hamma
To naji.
Haka suka gama tayi wanka ta  sa kaya ta shiga kitchen ta dafa masu abinci ta ajiiye a kan dinning din.

Ta kunns turaren wuta gidan ya dau kamshi ta kunna kallo kuma tana kallon wani flim din india me suna *prem rathan daan payo*
Na salman khan da sonam kawai flim din burgeta yake yi.

Wajan la'asar ya dawo yayi sallama ta amsa
Sannu da zuwa
Youwa kawai ya fada ya sha mur dan yaga alama in yana mata dariya zata cigaba da raina shi ne.

Dakin sa ya koma yaga yadda ta gyara masa shi ta saita komai duk da shi din ma me tsafta ne yaji dadij hakan ga kamshi na tashi wanks yayi yasa jallabiya yunwa yake ji dan rabon shi da abincin kirki tun jiya
Hamma kazo kaci abinci kaji
Ina wasa dake
Uhm uhm amma pls
 Kar ka yi wa kanka horon yunwa a kan fadan mu
Kai ya gyada ya raba ta gabsn ta ya wuce ya debi abincin da  kan sa yaci.
Yaji dadin abincin sossai ya sha lemo ya tafi palo
Duk abunda yske yi kallon sa kawai take yi burgeta yake yi.

Kawai jefa masa tambaya tayi hamma in tambayeka?
Uhm
Hamma kasan waye mahaifina?
Kallon ta yayi me yasa kike tambaya ta?
Kawai ji nayi ina sha'awar sanin ko da sunan sa ne

Kallon ta yayi cike da mamaki
Hamma ka fada min koda sunsn shi ne nima ina sha'awar sanin mahaifina ksmar kowa i feel lonely without him

Mikewa ysyi nima bsn san shi ba dan bani da imformation ksn mutanen duniya i just care for my self ya hau steps.

Hawaye suka zubo mata a fuskarta tana kuka biyu ne kuksn rashin uba da kuksn rashin miji ko da tana da mijin bashi da amfani a gunts tunda baya son ta baya kulata kuma be damu da damuwarta ba me son ka ai yana kula da kai da abunda ya shafeta ta hada kai da gwiwa tana kuka

Yana labe jikn kofa yana kallon ta zuciyar sa tayi sanyi tausayin ta ya kama shi amma bazai iya rarrashin ta ba.

 A nan bacci ya dauketa seda za ayi magrib yaxo ya tasheta tayi sallah.

***
Yusuf ya
Lafiya lou ya kake ya matsr taka
Lafiya kalou ya aisha humaira?
Tana lafiya
Dazu fa mutuniyar tamin wata tambaya wadda ta dan sa na tausaya mata
Tambayan me?
Cikin shekarun nan da dama bata taba tambayar mahaifin ts ba se yau
Subahanalahi
Me ka ce mata ksi ?
Kawai na kawar da zancen ne dan bsn san mezan ce mata ba.

Good ka shareta kaji
To dama in ban shareta ba ya zan yi da ita
 To se anjima
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
AISHA HUMAIRA
✨✨✨✨✨✨✨
*Na*
*Khairat up*
*45-46*

Wayyo Allah na shiga uku
Hamma!hamma!hamma!
Da sauri ya mike ya yi waje jin ihun aisha a kasan step ya ganta rike da kafarta goshin ta ya fashe yana dan zubda jini kadan kadan
Ya salam!garin yaya hakan ta faru humaira?
Tana kuka cikin shasheka ta nuna masa kafarta hsmma nayi targade kalli ya kumbura kuma kaina ma naji ciwo ka taimaka min zafi wallahi

Ya isa shh ya isa garin yaya kika ji ciwon?
Hamma na zo zan hau sama kawai nayi missing step se kafata ta gurde shine na fado kasa na buge kaina ma
Ta fads tana share hawayen ta
Daukarta yayi ya nufi saman da ita kin tsaya kins tunsnin ba gyara ba dalili dama yazaki ga hanya
 Ni ka daina min fada ka barni naji da daya tukun da zafin zanji ko da fadan ka ta fada masa tana murguda masa bakinta

Sakinta yayi a kasan tiles din saman
Wayyo Allah na shiga uku se Allah ya saka min
Kin cika min kunne da surutu kiyi shiru ko naki baki treatment din
Bakin ta ta rike da hsnnun ta hawaye ns zubo mata
Zaki ga mugunta ai dakin sa ya kaita ya kwantsr da ita kan gado
First aid box ya dauko ya dauko wani spray ya fesa mata a kafar tayi yar kara yasa hannun sa yana matsa mata kafarta kuka ta dinga yi masa amma dannawa yake da gayya daga karshe ya murda kashin yayi kara ta riko colar din rigarsa tana ihu wash
Hamma kayi a hankali wallahi Allah da zafi.

Spirt ya shafa mata a kan yasa mata bandage ya yi kwanciyarsa a gefen ta.

Kin dameni fa mslama da kuka ban san kuka kiyi min shiru ko na ksi ki waje na kwantar
Wannan ai rashin imani ne ya za ayi mutum yaji ciwo ksns masa masifa?

Kina hauka ko nine mara imanin da kika samu na taimaka miki ko to za a kuma stand up and get out to hell with you
Ba inda zanje
To fine ni zan fita ya dauko filon ya kwada mata a kai ya danne kafar sanan ya fice daga dakin die alone ya fada yana banko kofar

Mugu kawai se Allah ya saka min ta share hawayen ta kuksn maraici take yi yau Allah sarki dada da kina kusa dana ga gata


Dakin gefen dakin sa ya koma ya kwanta amma baccin ya gagare sa,ya dinga juyi ya kasa sukuni se tashi yayi yayo alwala ya dinga sallah ko ya samu saukin zuciyar sa.

Ita ma csn baccin ta kasa ga radaddi na damun ta ga ishi ruwa na damunta ranar tayi kuka daga karshe tace zan rama masdook muhammad zan rama

***

Baffa,dada,
Na'am yusuf
Dama baffa nazo da wata shawara ne
Uhm muna jin ka
Baffa meze hans a fadawa humaira waye mahaifinta a sansr da ita cewa *YAR WAYE JADAR DA IMILI*)
me yasa kace haka?
Saboda jiya humaira tayi wa masdook tambayar cewa waye mahaifinta koda sunan sa ne a fada mata

Ita aisha humsira din ce ta tambayi masdook babn ta?
Eh dada ni a gani na a fada mata komai ta ksi lokacin ai

Bana son gamuwarta da wannan mutumin ne shi yasa ai da ya damu da ita shekara da shekaru be zo ya nemi diyar sa ba wane irin uba ne shi tayaya humaira dan rashin hankali zata tambaye shi bayan be damu da ita ba

Dada kin dai san cewa da da mahaifi se Allah ita ma tana sha'awar sanin mahaifin ta tunda tana ganin kowa da nasa

To yusuf wane irin gata ne ba a mata ba ?
An yi mata dada amma ba kamar na mahaifinta ba

Yusuf a bar maganar nsn dan bana son ana maganar wannan mutumin domin kuwa tuna min yake yi da mutuwar *AISHA* kar ka fama min ciwo na da na danne a zuciysta da kyar

Shi kenan dada Allah huci zuciysr ki amma ki duba lamarin nan kar tarihi ya maimaita kan sa

Shiru ya biyo bsya kuma baffa yace yusuf haka ne zamu duba jeka Allah maku albarka amin se anjima youwa ka gaida amira zata ji
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*aisha humaira*
✨✨✨✨✨✨✨
*Na*
*Khairat up*
*47-48*

       Takaici ya isheta zama guri daya da tayi ba wani motsi tsaki tayi ya fi a kirga

Leqowa yayi dakin ke zan tafi aiki kin sha maganin?
Dame zan sha ban ci abinci ba
Au to me kike jira kici mana
Amma dai hamma wannan ai rashin tausayi ne
Au Allah na shiga uku abun mamaki mun yi dake dama cewa zan ji tausayin ki wai har kin gaji da game din?

Ai rashin lafiyar mutum tafi komai wane irin game ana ta rai

Kinga sena dawo in kin matsu ki samu abunda zaki sa a cikin ki ayyuka sun min yawa bazan iya zama gadin ki ba dama dai ina son ki ne ko da 1%ne da sena daure na kokarta na taimaka miki saboda ina tausayin Aisha humaira yayi ficewar sa .

Takaici ya isheta kukan ma yaki zuwa sena zuciya wanda yafi ciwo ita ga raki in tana ciwo wajan sha biyu da taga babu sarki fa se Allah seta lallaba ta tashi tayo wanka tana yi tana kuka
Da kyar a hankali ta samu ta sauka kasa tana bin bango sannan ta shiga kitchen din ta dafa indomie guda biyu dai dai cikin ta.

A kitchen din taci abincin ta sha youghrt sannan ta zauna a falon tunanin da take yi mezata yi masa ita ma ta rama?
Can tayi dariya tana smiling .

_6:00_

Ya shigo cikin gidan beyi tunanin samunta a falo ba ya ce aa patient da kanta?wallahi ita ce fa da kanta ka dawo lafiya likita
Lafiya lou to masha Allah
A je ayi wanka dan se tsamin rana kake abunka da kai namiji kuma ka sha aiki ko kuwa
Hararta yayi ya kara gaba ta dan yi dariya kasa kasa.

Da daddare hamma nas yaxo gidan nasu ya taho mata da nama da gasasshen kaji guda biyu da fresh youghrt

Ba karamin dadi taji ba tun a ledar ta fara ci ta ce hamma kullum kaxo da daddare kaji ?
To kanwas zan na zuwa ni me zaki na tanadar min?
Komai ma zan tandar ma hamma amma pls kana zuwa ka dinga kawo ice cream ma mana ko.

To yar'uwa za ayi yadda kike so kar ki damu
Masdook ya aikin?
Wallahi alhmadulilahi .ya kuma aka ji da me jiki
Da sauki
To Allah kara sauki
Amin.
Gata nan ai kq shagwabata da kayan ciye ciye
Ai girman ta ne ina ji da wannan kanwar tawa fa a duk cikin kannena wallahi
To me kanwa.
Sun dadde suna hira wajan karfe goma da rabi ya dau harramar gida har aisha na masa tsiya kayi aure dan nasan da kana da mata da tun isha kana gida ba inda zaka kuma zuwa
Dariya yayi yana rike baki to sis zanyi tunda za a fara min gori zanyi kin ji ko
Gwara dai ksyi hamma muzo mu dance mu kwaso shoki  😝
Ohoh kina nsn da halin naki ko
Kar dai ki manta ran litinin zan zo muje buk din ki fara wahalhalun aikin makarantar ki dinga motsa kafar ki ko ta warke bfr then.

To insha Allah to seda safe Allah tashe mu lafiya
Amin.

*******************
 A gajiye ta dawo daga makaranta dan sun fara lectures din a gajiye take sossai ta kwanta kan kujera me two seater
Kamar an mitsine ta tashi tayi window ta leqa taga hmma ne ya dawo kuma waya yake yi da sauri ta shiga kitchen ta dauko mai ta zuba kan steps tayi maza ta koma ta kwanta

Be jima ba sossai ya shigo cikin gidan da sallama
Ta amsa da fara'a tana murmushi
Ya kalleta kusan sau biyu ya kuma kallon ta
Aisha wannan devlish smile dinki fa ban yarda dashi ba
To kar nayi murmushi kenan saboda kar gaban ka ya fadi 😏
Hmm tafiya ya soma ya na hawa step din ya na hawa na biyar kawai santsi ya kwashe sa ya fado kasa ta bayan sa ya rike ya soma salati yana kiran sunan Allah da sauri ta karasa gunsa tana fuskar tausayi
Lah hamma garin yaya ka fado haka subahanallahi ta lallaba ta tashe shi suka shiga dakin kasa dan bazata iys zuwa sama dashi ba ya mata nauyi

Kwantar dashi tayi kan gado tana masa sannu ta gyara masa kwanciyar sa dukwani abu da ya mata jiya tayi masa ita ma kawai tayi ficewarta.

Gaba daya bayansa zafi yake masa Allah sa be samu fracture ba a bayan sa .

Wayarsa dake cikin alhihun sa ya dauka ya kira nas

Da sauri ya zo gidan ya same shi yadda ya ganshi yasa yayi saurin fita dashi ya kai shi asibiti.

A nan kuma hankalin humaira ta tashi ta dinga kuka wayyo Allah daga wasa abu ya zama babba.

 Allah kasa ba abunda ya same shi Allah kasa ciwon karami ne ta kasa sukuni.

A can asibitin aka masa treatment amma yana bukatar bed rest na sati daya a gida

Ya samu fracture minor a bayan sa amma yanzu an masa allura ya kwanta ya huta .

A waya ya fadawa humaira an basu gado innalillahi wa'inna illahir rajun hamma bara naxo aa ki zauna zuwa anjima zan zo wallahi hamma bazsn iya zama ba bazan iya kwanciyar hankali ba ban ganshi ba.

To zan zo na dauko ki to hamma ina jiran ka
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*aisha humaira*
✨✨✨✨✨✨✨
*Na*
*Khairat up*
*47-48*

       Takaici ya isheta zama guri daya da tayi ba wani motsi tsaki tayi ya fi a kirga

Leqowa yayi dakin ke zan tafi aiki kin sha maganin?
Dame zan sha ban ci abinci ba
Au to me kike jira kici mana
Amma dai hamma wannan ai rashin tausayi ne
Au Allah na shiga uku abun mamaki mun yi dake dama cewa zan ji tausayin ki wai har kin gaji da game din?

Ai rashin lafiyar mutum tafi komai wane irin game ana ta rai

Kinga sena dawo in kin matsu ki samu abunda zaki sa a cikin ki ayyuka sun min yawa bazan iya zama gadin ki ba dama dai ina son ki ne ko da 1%ne da sena daure na kokarta na taimaka miki saboda ina tausayin Aisha humaira yayi ficewar sa .

Takaici ya isheta kukan ma yaki zuwa sena zuciya wanda yafi ciwo ita ga raki in tana ciwo wajan sha biyu da taga babu sarki fa se Allah seta lallaba ta tashi tayo wanka tana yi tana kuka
Da kyar a hankali ta samu ta sauka kasa tana bin bango sannan ta shiga kitchen din ta dafa indomie guda biyu dai dai cikin ta.

A kitchen din taci abincin ta sha youghrt sannan ta zauna a falon tunanin da take yi mezata yi masa ita ma ta rama?
Can tayi dariya tana smiling .

_6:00_

Ya shigo cikin gidan beyi tunanin samunta a falo ba ya ce aa patient da kanta?wallahi ita ce fa da kanta ka dawo lafiya likita
Lafiya lou to masha Allah
A je ayi wanka dan se tsamin rana kake abunka da kai namiji kuma ka sha aiki ko kuwa
Hararta yayi ya kara gaba ta dan yi dariya kasa kasa.

Da daddare hamma nas yaxo gidan nasu ya taho mata da nama da gasasshen kaji guda biyu da fresh youghrt

Ba karamin dadi taji ba tun a ledar ta fara ci ta ce hamma kullum kaxo da daddare kaji ?
To kanwas zan na zuwa ni me zaki na tanadar min?
Komai ma zan tandar ma hamma amma pls kana zuwa ka dinga kawo ice cream ma mana ko.

To yar'uwa za ayi yadda kike so kar ki damu
Masdook ya aikin?
Wallahi alhmadulilahi .ya kuma aka ji da me jiki
Da sauki
To Allah kara sauki
Amin.
Gata nan ai kq shagwabata da kayan ciye ciye
Ai girman ta ne ina ji da wannan kanwar tawa fa a duk cikin kannena wallahi
To me kanwa.
Sun dadde suna hira wajan karfe goma da rabi ya dau harramar gida har aisha na masa tsiya kayi aure dan nasan da kana da mata da tun isha kana gida ba inda zaka kuma zuwa
Dariya yayi yana rike baki to sis zanyi tunda za a fara min gori zanyi kin ji ko
Gwara dai ksyi hamma muzo mu dance mu kwaso shoki  😝
Ohoh kina nsn da halin naki ko
Kar dai ki manta ran litinin zan zo muje buk din ki fara wahalhalun aikin makarantar ki dinga motsa kafar ki ko ta warke bfr then.

To insha Allah to seda safe Allah tashe mu lafiya
Amin.

*******************
 A gajiye ta dawo daga makaranta dan sun fara lectures din a gajiye take sossai ta kwanta kan kujera me two seater
Kamar an mitsine ta tashi tayi window ta leqa taga hmma ne ya dawo kuma waya yake yi da sauri ta shiga kitchen ta dauko mai ta zuba kan steps tayi maza ta koma ta kwanta

Be jima ba sossai ya shigo cikin gidan da sallama
Ta amsa da fara'a tana murmushi
Ya kalleta kusan sau biyu ya kuma kallon ta
Aisha wannan devlish smile dinki fa ban yarda dashi ba
To kar nayi murmushi kenan saboda kar gaban ka ya fadi 😏
Hmm tafiya ya soma ya na hawa step din ya na hawa na biyar kawai santsi ya kwashe sa ya fado kasa ta bayan sa ya rike ya soma salati yana kiran sunan Allah da sauri ta karasa gunsa tana fuskar tausayi
Lah hamma garin yaya ka fado haka subahanallahi ta lallaba ta tashe shi suka shiga dakin kasa dan bazata iys zuwa sama dashi ba ya mata nauyi

Kwantar dashi tayi kan gado tana masa sannu ta gyara masa kwanciyar sa dukwani abu da ya mata jiya tayi masa ita ma kawai tayi ficewarta.

Gaba daya bayansa zafi yake masa Allah sa be samu fracture ba a bayan sa .

Wayarsa dake cikin alhihun sa ya dauka ya kira nas

Da sauri ya zo gidan ya same shi yadda ya ganshi yasa yayi saurin fita dashi ya kai shi asibiti.

A nan kuma hankalin humaira ta tashi ta dinga kuka wayyo Allah daga wasa abu ya zama babba.

 Allah kasa ba abunda ya same shi Allah kasa ciwon karami ne ta kasa sukuni.

A can asibitin aka masa treatment amma yana bukatar bed rest na sati daya a gida

Ya samu fracture minor a bayan sa amma yanzu an masa allura ya kwanta ya huta .

A waya ya fadawa humaira an basu gado innalillahi wa'inna illahir rajun hamma bara naxo aa ki zauna zuwa anjima zan zo wallahi hamma bazsn iya zama ba bazan iya kwanciyar hankali ba ban ganshi ba.

To zan zo na dauko ki to hamma ina jiran ka
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨
*Na*
*Khairat up*
*49-50*

   Kasa sukuni tayi kwata kwata komawa daki tayi ta zsuna jigun tana tunani kala kala ta kasa nutsuwa ji take kamar wani abu ze faru da hamma ta dinga kuka

Dare yayi bata ga hsmma nas ya shigo ba ta kira sa a waya be dauka ba ai se gaban ta ya dinga bugawa ta kasa sukuni kwata kwata

Saukowa kasa tayi ta zauna a falo tayi zugum taji bugun kofa da sauri ta yi gaba tana kuka tana budewa taga hamma nas da hamma masdook a jikin kofa yana rike dashi

Da sauri ta taimaka masu suka shigo ciki,daki suka kaisa ya kwanta
Sannu hamma a fakaice ya dalla mata harara dan yasan ita ce tayi sanadin faduwar sa daga kan steps.

Hamma nas ya mata bayanin magunguna da yadda zata na masa gobe zsn dawo nasan kina da lec sena zauna kije ki dawo tana shsrbe hawaye tace aa ni ba inda xan iya xuwa se hamma ya warke
To shi kensn se da safe Allah tashe mu lafiya amin.

Dawowa tayi ta xsuna gefen sa dan Allah hamma ksyi hakuri bsn dauka ze zama serious ba haks kayi min afuwa hamma

Ki bar min daki dan zaki iya kashe ni ma

Innalillahi wa inna illahir rajun dan Allah kar ka fadi haka wallahi wasa nake

Ni abokin wasan ki ne ? Min taba wasa dake ?
Wallahi in bski bar min ganina ba sena yi maganin ki duk sanda na tashi mara d'a'a kawai *get out*ya fada da tsawa jikin ta har 'bari yake dan tsoro ta mike ta fice waje

Dakin ta koma ta fashe da matsansncin kuka da kyar bacci ya dauke ta.

Da safe ta koma duba lafiysr jikin sa amma taji kofar a kulle wato ya kulle kenan karta shiga wata zuciyar tace mata kema banza ce mara zuciya kin manta abunda ya miki kema just get ready and go to ur skul.
Ki nuna masa rashin da'ar da yace baki da ita.

Wanka tayi.tasa kayan ta hijab ta saka ta dau jakarta a hanysr fita taga hamma nas ya dawo

Ina zuwa?
Makaranta na manta ina da test,
To a dawo lafiya
Allah sa
Ya mika mata dubu biyu ta amsa tayi gaba dan dama bata da isassan kudi a gunta.

Cikin gidan ya shiga jin dakin a kulls yasa ya buga masa kofar nas ne bude
Yans jin haka da kysr ya mike ya bude masa
Me na kulle daki kuma?
Kawai an tashi lfy
Lafiya lou
Ya jikin?
Alhamdulilahi

Ka sha maganin?
Uhm'uhm
To why?
Ban karya bane
To amma ka bari matar ka ta tafi oll well kuwa masdook?
As in?
Tsakanin ka da aisha nske tambayar ka!
Yes man
Mesa ka tambaye ni?
   Saboda wannsn canjin na tare daku kamar ba couples ba
  Haka dai kace
Uhm masdook ka daina boye min nasan komai ba normal bane tsakanin ku amma in tayi tsami maji
    Hmm kaji alheri!
Abinci ya siyo masa ya basa sannsn ya bashi maganin ya taimska masa yayi excersing din jikin nasa sannsn ya taimska masa yayi wanka yana wajen toilet din.

A ajin lectures din take amma hankalin ta na kan hamma masdook ta kasa nutsuwa kwata kwata tunani take ya jikin hamma yake ta barsa shi kadai waysr hamma nas ta kira

Hello hamma
   Hello
Hamma ya jikin nasa ?
Da sauki alhamdulilahi.
To se anjima
To.

Se biysr ta gama lec ta koma gida hamma nas a falo yana kallo gefen sa masdook ne shima yana aiki ta laptop tayi sallama ta shiga ciki amsawa suka yi
Hamma ya me jiki?
Da sauki Allah bada lada amin ya Allah
Ni zsn wuce ga amanar ki nsn na baki se gobe
To hamma Allah kara zumunci
Amin.

Shiru falon da ga karshe ta shiga kicin tayi miyar ganye ds tuwon shinkafa ta kawo masa kan tebur

Dauke tsiyar ki dan ke makiyata ce who knows ko kin zuba min guba a ciki

Hawaye suka saukar mata a fuska hamma yazan sa mska guba fisabililahi

Zaki iya mana tunda kika yi sanadin zama na a nan zaki iya komai ma.

Dan Allah kayi hakuri wallshi ban yi da niya ba
Kinga ki kwashe tsiyar ki nagode bana so.
   Shi kenan kar ka ci ina ruwana ka mutu din seme kai ka jiyo ta dauke kwanon abincin ta koma daki.

Ta fada kan gadon ta na kuka.

Ganin haka ta koma daki yasa ya dau stick ya shiga kicin ya dauko abincin ya koma falo yaci ya koshi ya sha magani ya kwanta a kan kujerar.
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*Aisha humaira*
✨✨✨✨✨✨✨
*Na*
*Khairat up*
*52*


_ina mai baku hakuri kan rashin typing da wuri bana samun tym ne ina baku hakuri_

Bayan tafiyarta ya ga zaman bazai masa ba ya shiga ko zaiga abinci kan wani table dake cikin kicin din ya shiga ya buda tiffin din na saman kawai ba komai ciki na biyu kuma note ne a ciki ya buda yaga abunda ke ciki
    _hamma ka daina fushi da abinci in xaka yi kayi fushi da ni kadai ka cancanta ka nuna fushin ka gareni nasan bayan na tafi kana jin yunwa but bazaka tambayeni abinci ba saboda ego dinka amma na ajiye maka abincin saboda bsn son kana salalabawa cikin kicin da daddare kana daukar min abincina boye,pls kaci ka sha magani am not there but am there with u in my heart ko da kai baka sona ka sani ni ina son ka_

Murmushi ya kubuce masa ya dauko tiffin din da plate ya zuba abincin chips ne da kwai a cikin karamin flask kuma ruwan tea ne
Ya zsuna ya gama ci.
   Yana fitowa ya ga nas a falo xaune yana jiran sa mr.lover!
Hmm,wa kenan?badai ni ba ya nuna kan sa
Uhm muje nide a duba ka yau check up za a yi.

To muje .

***

Bayan sun gama ne ya ce ma nas muje ta makarantar yarinysr nsn mu dauko ta
 Ta gama lectures din ne?
I think so
Kirata dai muji dai kar muje she is not done.

Kiranta yayi lokacin suna aji suna daukar darasi na chem taji vibration daukowar da zata yi taga wake damun ta taga nun.
 *mr.arrogant*
Ta gwalalo idon ta waje cike da mamski a ranta tace look who is calling da sauri ta dauka ta kara a kunnen ta tana tsugunawa dan kar ta damu na kusa da ita
Hello ta fada ya jikin badai matsala ko ?
Ta tambsye shi a tare
Ya ce shhhhhh! kin gama lectures din ne?
Tayi jim sai kuma tace eh na gama
Owk ki jira ni gani nsn zuwa yau tare zamu tafi gida
 Hamma baka da lafiya fa wa ya ce kayi tuki kuma pls ka zauna a gida in kaji sauki seka fara tuki amma ur back is still.....kin fiya surutu tare da nas muke
Hmm ta fada tana ajiyar zuciya to sekun karaso.

Aisha humaira ko surutun tsiya bata bsri mutum ya gama maganar sa zata katse mutum da tambayoyi.

***
Kwatancan inda take ta masu a nsn nas yayi parking
Gogan yana daga cikin mota ya zugi tagar yana kallon wajan yadda mutane suka yi yawa a gurin musamman maza wani abu ya tsya masa a rai.
Mtsw .

A bakry ya tsaya yayo masu siyayya sannan ya sauke su a gida.



*53*

Be shiga ba ya barsu a nan ya koma gidan sa.

   Tsoron kama shi take yi kar ya mata tsawa jikin ta na rawa ta riko hannun sa kamar ze kwace se kuma ya barta ta taimaka masa ya riko ledar a hannun sa bude kofae tayi sannan ta shigar dashi.

Hamma zaka daki ko na barka a falo?
  Kmar me koyon magana yace barni a nan kunna min tv kisa min gun kwallo
Tom
Seme?
In anjima in ana da bukatsr wani abu zan kira ki amma tukuna bani ruwan lipton me dan citta a ciki.

A flask dan karami ta kawo masa ta ajiye
Da dan karamun cup to na taya ka kallon?
  Wani kallo ya mata aiko tasa dariya ta koma dakin kusa da falon ko zai kirata.

Murmushi yayi.kawai ya dauko cup din ya zuba tea din yana sha.
   Kallon champion league yake.

Har kusan karfe hudu yana kallon daga bisani ya mike yayi sallah sannan ya shiga dakin da take ta fito daga wanka kenan daure da towel ta yafa daya kan kafadar ta.
  Ganin an bude kofa yasa ta bi kofar da kallo duk da tasan waye amma bata yi tunanin cewa zai shigo ba din.

Kallo ya bita da shi sama zuwa kasa yadda lemar ruwa a jikinta
Lumshe idanta tayi zarazaran gashin idan ta ya kwanta a fuskarta
      Tsayuwa gagarar sa tayi kamar ya tsuguna a kasa haka yaji kawai ya saisaita ksn sa ki..hada..min...ruuuuwa...zan..yi...wankaaaa......

To ta fada murya na rawa
Ficewa yayi da bangon dakin ya jingina yana maida numfashin sa

Doguwar riga tasaka iyakarta cinya da sani pencil din wando pink rigar kuma yellow.

Ta daura pink din  dankwali ta fita dakin sa ta shiga ta hada masa ruwan ta zuba masa turare a ciki
Sannan ta sauka ta fada masa hamma na hada maka ruwan
To sannun ki
Muje man ki taimaka min na haw samsn ko bazaki iya ba?

  Aa zan iya mana in zaka yarda ai umarnin ka nake bi kai ka hanani kusantar ka kar na maka illah.

Hmm kin fadi gaskiya kin ce wani abu amma muje dai
Kugunta ya riko da karfi sossai yana jin kamshin jikin ta da kyar ta saisaita nutsuwarta ta taimaka masa ya shiga bandakin nasa kamshi ya doki hancin sa

  Besan sanda ya janyo ta ba jikin sa ya rungume ta tsam kamar za a kwace masa ita sumbatar ta ya fsra yi ksmsr wani mayunwacin zaki gaba daya bata da laka dan kan sa ya cikata ya hankada ta waje tangatanta tayi kamar ta fada kasa ta rike handle din kofar.
   Ta bisa da kallo kallon ka raina min hankali
 Shi kuma kallon amfanin ki kennsn a guna ya mata
Hawaye suka zubo mata a ce ayi rayuwa a haka.

Kofar ya banko da karfi ta ji abun har tsakar kanta
Lallai zan gyara maka zama ni bazsn dau wannan wulakancin ba ta share hawayen ta sannsn ta koma dakin ta.
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
AISHA HUMAIRA
✨✨✨✨✨✨✨
*na*
*khairat up*
*54*

Aisha ! Aisha ! Aisha ! Sau uku yana kiran ta bata amsa ba
A'ah'ah ! Ina ita kuma wannsn ta shiga?
  Leqowa yayi ya ga tana falon a zaune waya ma take
Aisha! Ta dago ta masa wani kallo amma fa gaban ta na faduwa sossea dan bata san meze biyo baya ba
Amma de ke baki da mutunci kina ji ina daga murya na daddage ina kiran sunsn ki amma kika min kunnen uwar shegu?

Bazan zo ba din ni ba baiwar ka bace
Ya harde hannun sa a kirjin sa ya na kallon ta owk,yayi kyau kin girma ko ?
Ni kike fadawa wannan maganar ?
An fada maka din nace an fada mika din do ur worst
Dariya ma ta bashi shi kam look ki daina min wani kurin banza dan abunda ke cikin zuciyar ki bashi ne a bakin ki ba kar ki dau dabi'ar da ba taki ba.

So kindly zo nan ki gyara min dakina zan huta
Wallahi kaji na rantse da Allah bazan motsa daga nan ba especially don yin aikin ka

Mamaki ya cika shi
Cikin kuka yaji tana cewa na gaji da wannsn rayuwar na gaji da mutuwa kadan kadan me makon na dinga rayuwa cikin fargaba da tsoron kas better na rabu da kai na gaji da wannan *cin fuskar* na gaji da *son maso wani*
Na gaji da halin ko in kula da kske nuna min ni da gaske da zuciya daya nake zaune da kai ban yi tsamanin zaka sakawa familyn mu da wannan abun ba matsayina na jikar dada wadda ta muku alheri ta maida ku tamkar jinin ta amma kake wahalar dani baka dubi maraicina ba
 Ta tsuguna a gurin ta fashe da kuka cikin jan majina tace in dai jikina kake so gashi nsn naka ne amma why not da soyayya? Why da kiyayya?
Amma na daina kuka ta share kwallar ka na share kwallata na daina sa kaina cikin *yanayi* na wahala marar misaltuwa hamma masdook dikko na gaji da sa *rayuwa ta* cikin tunanin yaushe zaka soni?yaushe zaka rungume ni cikin love yaushe zaka *amince* dani da zuciys daya a matsayin matar ka hamma wallahi tallahi na gaji dan Allah dan girman nabiyi rahmati dan son ka da iyayyen ka hamma ka sauwaka min zan koyawa kaina daina sonka zan yi kokarin *moveing on* amma dan Allah ka sake ni!!!!

A nan yaji jikin sa yayi sanyi tausayinta ya ksmashi ya nanata kalmar saki sau uku yana jijjiga kan sa.

Hamma dan Allah ka sake ni wallahi na gaji na yarda na yi failing kayi winning ve lost the game amma har abada bazan daina sonka ba ni na sani amma ka sakeni
Me za ayi da rayuwar aure mara dadi da caring irin auren mu tun ban san so ba hamma nake kaunar ka hamma memakon ka dubi zuciyata ka dubi girmsn da kake dashi a guna ba abunda bazan iya saboda kai ba amma.....

Na tsani wannan zuciyar tawa wadda bata min adalci ba na shiga cikin *hatsaniyar so*inda na hadu da *takaicin namiji*

Saukowa yayi yana jin maganganun ta da suke shiga kansa  suke ratsa ko ina na jikin sa haka kawai wni abu yake jsn sa gareta tamkar magnet yana attracting dinsa.

Har yaushe mace zata samu 'yanci gun namiji?
Har yaushe mace zata daina fuskantar wulakancin d'a namiji?

Besan sanda ya rungumeta ba tightly yana shafa bayanta yana shafa ksnta da daya hannun sa shhhh ya isa easy kiyi shiru pls ki daina kuka relax relax calm down ki daina zubda hawayenki saboda masdook am...se kuma yayi shiru ita kuma bata daina kuksn ba kuma turaren sa ya sa mata kasala tana kokarin kwacewa ya dada mata rikon *am sorry* ya fada first in life kuma a gun mace hankade shi tayi karya ne duk karya ne kar kayi kokarin consoling dina dan nasan is some kind of ur planning
  The grate.masdook muhammad dikko mr.arrogant yace ayi ha'kuri is next to impossible
Dakin ta ta shige ta banko kofar dakin akwatin ta ta dauko ta zuba kayan ta a ciki ta fito daga dakin tana kuka ta dau wayarta zata yi waje ya riko akwatin nata da hannun ta ya ma manta da ciwon dake jikin sa ya mata wata iriyar cafka
Me haka humaira?
  Humaira ina zaki ? Ki duba fa ki dubi ni nine masdook ki dubi yadda nake baki hakuri wanda ban taba bawa wata 'ya mace ba a *rayuwata* se a kan ki ni kaina ban son dalili ba da naga hawayen ki se naji zuciyata na suya bakin ciki ya kama ni raina ya baci ban iya holding din kaina ba na kawo kaina gareki
Kar ki min haka dan Allsh kar ki fita kin manta alkawrin da kika min
 _ni naki ne kuma dole na soki?_
Kar ki fita daga *rayuwata* ina.....
Hamma ka kyale ni bani da amfani a gareka saboda jikina kake so ni kuma baxsn baka ba saboda ba ka kaunata ni ko mezsn da kai?

 Ohh ya fada don kalaman sa sun fara karewa dan bema san daga ina suke zuwa ba ya dafe goshin sa tayi yunkurin ficewa ya dad'a riko ta haba humaira ta humairan dada humaira ta masdook
   Rungumeta ya kuma yi da karfi humaira look at me ya riko fusksrta kalli cikin idanuwana humsira me kika gsni a cikin su?
      Dagowa taki yi humaira look at me!ki kalle ni harda tsugunawa kasa humaira ki min hakuri ki min afuwa in kika tafi kika barni ai baxn kuma samun irin ki ba na yarda na sani kina sona kina kaunata kuma na kasa ganewa humaira dubi yadda na zamo
  Ki yafe min humaira ki yarda da ni kin san cewa ni ba karya zan miki ba dan bana yi kin sani hanun sa cikin nata
  *ki yarda da abunda zan fada miki nasan ni me laifi ne a gareki ban san kina da muhimmanci a guna ba se yanzu da kike kokarin barins humaira ke haske ce a rayuwata me haskakka ni humaira ni me kishin ki ne me kaunar ki ne ina son ki kuma yanzu na dadda yrda ba wadda zata soni kamar ki ba wadda zata kaunace ni kamar ki ba wadda zan daraja kamar ki dama ance baka san muhimancin rasa abu ba me muhimmanci a gareka ba seka ga wannan abun ya nisance ka ni baxan yi wannan gangancin ba humaira _trust me_i love you*

👀 idanta da suka rine dan ja ta dago ta sauke su a kan sa cike da mamaki
  *yes ina sonki*

No!no!no! 🙉 wannsn wani game din ne naka wata hanya ce xaka bi don yaudarata dan bakanta min dan sani a cikin kuncin rayuwa ni bazan taba  yarda da wannsn magansr taka ba masdook bazai taba son wata ba se kan sa u re selfish kan ka kawai kake so da ka'idojin ka da ra'ayin ka damuwar ka kawai ka sani baka san ta wani ba don haka yau za bar ma gidan ka.

 Duk mai laifi a baya in ya dawo ya nemi afuwa ai baza aki amsa ba sai a bashi wni chance din dan yayi prooving kan sa ki bani wannan damar humaira ki bani damar nuna miki matsayin ki a gareni .
Humaira
_thd forgiver is greater than the purnisher_
Ke amanace a gsreni kar ki bari na kasa rike amanar
 Amana hamma wannsn kalamar sam bata dace ts fito daga bakin ka ba dan ba ka san ta ba
Da ka santa da baka cita ba

Innalillahi wa'inna illahir raji'un !  Humaira mezan yi dan na nuna miki cewa na tuba ina sonki ina kaunar ki a ksnki yau ni har hakuri na bada nayi rarrashi na yi kwalla kuma me kike so na kuma miki ki yarda cewa ina  sonki

Shiru ta masa ta kwace hannun ta don't touch me kyale ni
     To naji baxan taba ki ba amma pls ki maida kayan nan cikin daki kinga ni msra lafiya ne ina bukatar hutu amma kin sa na yi tsayuwa da tsuguno ki tausaya min

Jakar ta kwace ta juya ta koma daki daga bakin kofa tace masa kar ka kuma damuna kowa yayi zamsn sa as u said kuma yes ka fadi daidai i regret loving u and knowing you congratulations u win
Ta kullo masa kofar a fuskar sa

Zaunawa yayi ksn kujera mugun mamskin ksnsa yake karshe ya kasa nutsuwa shin meya same ni? Mtsw kai mata matsala ne sanda ake son su lokacin suke nasu shaksra din

Ashe tana jinsa ta fito dauksr wayarta tace
*ai ku din ma matsala ne* tayi komawarta
  Dariya ta bashi ya dinga smiling shi kadai yana cizar leben sa.
  A ransa yace *love* ko ciwon kai
 _Aisha humaira i like you i like you style i like ur attitude i like ur evrything bsn san sanda sonki ya min kamu ba a jikina da ma jinina kin zamo jini me yawo a jikin masdook_
Kamar _yadda kike fada min mr.arrogant yes i am amma mr.arrogant ya zama mr.lover_

  *barkan mu da safiya Allah sada mu da alkairin wannan ranar amin*
[6:26PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA
✨✨✨✨✨✨✨
*na*
*khairat up*
*55*

Kan gado ta kwanta hawaye na bin wani se gogewa take yi ta rasa kukan me kuksn dadi ne ko kuma kukan bakin ciki shin da gaske ne abunda hamma ya fada tabbas tasan hamma baya karya wata zuciyar tace ki tsaya kina biyewa namiji yana yaudarar ki baki san dadin bakin da namiji ba shi yasa kike fadin haka kin riga da kin gama matowa da son hamma
  No hamma abunda ya fada da gaske yake har zuciyarsa amma ni ban yarda ba sena gwada shi,ban gama yarda cewa yana sona ba ai ba haka kawai zan fada tarkon son sa sp easily ba dan kuwa hamma is a good planer
  Ringing din wayarta ya katse ta dauka tayi taga sunan amira a ciki
 Dauka tayi da hanzarin ta hello sis
Hello sister ya kike?
Lafiya lou ya me jiki kuma?
  Jiki alhamdulilahi
Ya gidan naku?
Gida lafiya lou
Ya hamma yusuf
Wallahi lafiya lou muna tunanin zuwa ma kanon cikin satin nan duba hamma
To muna jiran ku ki gaida  mutanen gidan za su ji se anjima yauwa.

Wanka tayi ta dubi agogo taga karfe goma sha biyu saura ta dafa kanta omg!ya zan manta da wannan lec din ga test ina da cikin gaggawa ta shirya cikin doguwar riga free fitet ta dau mayafi kashka pink ta dau jakarta ta yi waje.

Shima ya shirya cikin manyan kaya ys kalleta ina zaki humaira?

Bata ko kalle shi ba tace makaranta
    Au kina da lectures din rana dama kika kai haka a gida?
Uhm
To muje na sauke ki nima hanysr xanyi
Nagode zsn kai kaina
Kiyi hakuri na ksi ki kar ki kuma latti dan yanzu ma bata lokacin ki kike yi tunda kina min gardama da wannan surutun gwara muje na kai ki
A ranta tsyi nazari tana fa da gwaji .
To amma da sharadi daya?
Ina jinki ya fada ya amsa jakar hannun ta muje ina jinki muna tafiya bana so ki makara daidai lokacin ya kulle kofar gidan yasa cikin basket dake sakale saman kofar

Motar ya buda mata ta shiga tana wani shan kamshi tana cika tana batsewa youwa ina jinki me sharadin naki?
   Bazaka takurawa rayuwata ba kar ka kuma shiga harkata daga yau
  To naji amma yar kanwata yi hakuri amsa tissue din nan ki shsre wannsn kyallin na bakin ki
Yqnzu fa na fada maka sharadina
Ai naji kuma cewa kika yi daga yau ai yau din bata kare ba ko kuwa
   Hmmm sharewa tayi da tissue din haka ya dinga mata hira wanda seda tayi mamakin baki sa dan bata taba jin yana magana ba haka se yau har dep dinsu ya kaita ya mata se anjima ta sha kunu ta kulle masa kofar ta shige abunta
  Ya kwanta jikin motar yana numfashi kasa kasa lallai ina da aiki a gaba aisha zata wahalar da ni
Niko mezan yi na lallaba ta ?

Wa ya ga harara a duhu!

Haka ta gama lectures dinta kusan hour hudu tayi lec biyu take da ranar fitowar da zata yi da wata kawarta fatima ita ma amarya ce.
 Mamaki ya cikata dan ganin hamma masdook yana xaune a motar ya kwantar da kujerar sa yana kwance ya lumshe idsn sa
Ya dai kin san shi ne?
Uhm mijina ne
Oh ashe yazo daukar ki
Uhm
Knocking tayi masa a window din
Bude idan sa yayi ya juyo yaga waye zai katse masa jindadin sa.

Murmushi yayi wanda point dinsa ya loma ya bude mata kofar shiga tayi tace fatima shigo man mu sauke ki a gida
Aa ki barshi nagode my heart xai zo ya dauke ni yana hanya shi ma
Ok to se gobe
Allah tashe mu lfy
Amin.

 Reverse yayi ya kara gaba shiru motar ya juyo yana kallon ta humaira yanxu haka zamu yi rayuwa
Kai ka siya ayi hakan
Hmm amma nace ayi hakuri ko
Dan Allah ka daina takura min wallahi ina nadamar hakan

Hamma dan Allah ka bari kaji ka kyale min rayuwata ina cikin damuwa ka barni pls

Ok naji anjima se muyi magana
No bazamu yi ba kar ma ka fara kawai.ka sani ba ruwan ka dani

Hah wai ni ya kike so nayi da kaina ne?
Matsalar ka kuma wannan

Shi kennan humaira ba komai ai dan nace ina son ki shi yasa kike min haka amma zan hakura ki dinga min abunda kika ga dama amma zan shanye

Tsaki tayi
Juyowa yayi yana kallon ta tama dauka dukan ta zeyi kawai se taji shiru ya koma kan tukin sa.

Wanka tayi ta masu girki ta jera kam tebur bata masa magana ba ta debo nata tana ci shi kuma cikin wando short da riga yar karama ya karasa kusa da ita aa ba bismillah,ke kadai zaki dinga ci bani
Banza ta masa ya sa spoon cikin nata yana kokarin ci tashi tayi zata tafi seya kamo hannun ta ba kyau tashi daga gun cin abinci kamar kina insulting din abincin ne ki zauna muci kamar yadda muke ci da

Zaunawa tayi ta zauna suna ci shiru ba wanda yace uffan cikin su ruwa ya sha ya kware
Hankalin ta ya tashi ta dinga shafa masa bayan sa har ya lafa masa
Sannu hamma, sannu, kaima ksna shan ruwa kana wani abu daban
Laifin ki ne,
Laifina kuma?
Eh laifin ki
Kina kusa dani ne kinga yadda kika yi kyau shi yasa na shagala da kallon ki har na kware
Mikewa tayi ta koma falo
Kai ya girgiza kawai nasan yadda zan dake
[6:27PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*aisha humaira*
✨✨✨✨✨✨✨
*na*
*khairat up*
*57*

Washe gari data tashi daga barci ta wanke bakin ta tayi wanka ta daura zanin atampa ta gyara jikin ta dake ta tashi da ciwon mara
Dan ta girka abinci ta fita waje kawai ballons ta gani jajjaye shape din love da roses a kasan carpert din a kasa aka yi ado da flower me yellow ya rubuta
   *i love you Aisha humaira will you be mine*

Ya kulle mata ido ta baya
Me haka hamma ka rabu dani dole ne zaka dinga takura min
Shhhhh! Ya dora yatsan sa a kan lips din ta
Ya ja hannun ta zuwa cikin dakin sa
Kunce mata daurin yayi daga idan ta
Hotunan ta ta dinga gani ta ko ina manya manya window size an jera su a ko ina
 Bakin ta, ta bude cike da mamakin sa wai shin da gaske mutumin nan yake ?
Hamma waya maka wayanan abubuwan ?ka daina wahalar da kan ka ba su zasu sa na hakura na yafe maka ba ni na gama da babin ka
I just need space ka kyale ni all wayanan bazasu sa na damu da kai ba kamar da lokacin da na lallashe ka na nuna maka muhimancin ka a gareni ai baka yarda ba.shi yasa na ce maka kan ka kawai kake so.u re selfish wato kana nufin son ka shi ne so nawa was just rubbish? Hamma dan Allah ka daina wahalar da kan ka humaira bata sonka yanzu

Idan sa ya lumshe ya na kallon karamin bakin ta se zazzaga masa masifa take yi kawai ji yayi tsiwar ta ya burge shi

Ina magana hamma ksna kallona
Yes ke nake kllo saboda wani kyau kika kara da kina min wannsn tsiwar taki

Hmm!ok!to na gane me kake nufi na zama mahaukaciya ko?
    Hannun ta yaja cikin yan seconds ya mata abunda bata yi tsamani ba idanta kawai take blinking tana zare su dan kan sa ya cikata yana maida numfashi
  Da gudu ta fita waje
Shi kuma ksn gadon sa ya fada yana murmushi wayyo Allah na so da wuya yake kai jama'a dubi yadda na koma cikin kwana daya na zama mr.romantic harda aro tactics na malaman soyayya dan na samu ksn masoyiyata amma ta fiya taurin kai amma nima na iya taurin ksn zan lallabo ta

  Tana komawa dakin taga wata katuwar teddy ja da kuma wata yar karama rungume jikin teddy din an rubuta _i love u_
Humaira da teddy tayi smiling ta dau teddy din ta gyara masa zama ta kwanta kan gadon tana kallon saman cilin tana murmushi wow baxan manta wannan ranar ba tayi tsalle tana ihu da karfi da sauri ta toshe bakin ta au kar ya jini amma wannan hanyar dana bi ta hora hamma ita ce daidai am enjoying it alot

Gashi ta samu ganin other face na hamma masdook ya zama mr.lover din karfi da yaji abun ya burgeta flawers ,ballons,teddy,pictures abun kam ya mata dadi sossai kamar tace masa i love you to na yafe maka take ji amma bazata iya ba so take ta gama tantancewa da gaske ne yana son ta yanzu ko wani planning din sa ne again.

Lips dinta ta shafa yadda yayi laushi tayi smiling ta rungume teddy din i lyk it ta fada.

***

Kwanan shi hudu yana mata abubuwan mamaki da salo salo na soyayya wanda bata yi tunanin cewa ya iya su ba amma tayi biris da shi

Ransr na biyar ko ta dawo daga makaranta taga motar hamma yusuf a varander din waje da sauri ta karasa cikin gidan wani dadi taji ganin amira da fadima da hamma yusuf da hamma nas da hamma ni'imatullahi da hamma kamal
OMG!houseful gaba dayan ku kai amma.ina marhaba da zuwan ku
  Suka rungume juna ita da su fadima amma kun min baxata shi ne baku fada min nayi xamana ba a gida yau?

To da mun fada miki ya zamu ga wannsn expression din a face dinki?
 Wow wallahi naji dadin ganin ku sanunku ya hanya?
Alhamdulilahi ina kuka baro min dada ta?
  Dada na gida tana kewarki
Hawaye ya tarar mata a ido
 Allah sarki dada nima ina kewar ta nayi misin nata
   Tisssue ya mika mata mrs.cry amsa ke kuma kunzo zaku sa min mata kuka ko?
  Hamma nas yace lallai naga sauyi muda muka zo abin arziki shi ne za a mana kora da hali
Barshi hamma ai dan sun gan mu ne kar mu kashe musu jindadin kwana 2
  Au wai kwana zakuyi?
Ya fada da sauri
Aka sa dariya sossai humaira tayi kasa da kanta ta cusa ksnta jikn amira tana dariya kasa kasa
Gaskiya kuyi hakuri ku tattara ku koma gidan nas ni ina bukatar privacy da matata
   Hamma yusuf yace au Allah?
Eh mana!
To shi kensn tunda kace haka wallahi a nsn zamu kwana ke humaira jeki gyara mana dakuna guda uku na sama kin yi baki
   Wannsn ne kuma baka isa ba babu abunda zata yi kasa matar ka ta mska duk wanda ya matsu kuma yayi aure
Ni matata yar hutu ce
Ikon God
Se kallo inji hamma masdook
Ni'imatullahi yace aa meye zafi nikam zan bi nas mu tafi gidsn sa dan naga alama masdook baya son xaman mu a gidan sa kasan ango ne.

Ku dai kubi nas amma nikam.nan zan kwana sena rage masa jindadin kwana 2 nama fasa kwana dayan
Humaira dai tashi tayi ta shiga kichen dan masdook ya gama bada ita gun hamma yusuf
  Fridge ta bude ruwa ta dauko ta tsiyyaya a cup tana sha kawai ji tayi mutum ya riko kugunta ya hada da jikin sa yana shafa bayan ta  kiss ya mata a bayan ta lumshe idan ta tayi dan sakon ya isa gareta
Juyo da ita yayi ta yi maza ta kulle eyes dinta
  Pls ksr ki nuna musu we are not normal ki nuna masu komai ya daidaita a tsakanina dake dan Allah kar ki bani kunya i promise zan miki abubda kike so bayan sun tafi kinji amma ki bsni hadin kai yanzu mu kasance tare har se sun tafi mu dinga komsi kamar normal wife and husband duk da ni bani da matsala matsalar daga gunki take na baki hakuri kin ki ji na rasa mezan ce miki kuma humaira taurin kan ki yayi yawa.

  Hmm naji hamma amma ka cikani ba kowa a nan daga ni se kai seka bari se muna cikin su seka yi koma wane irin pretending ne amma banda yanzu i need freedom ban son kana taba ni haka wani.iri nake ji yadda kasan ana zuba min wuta a jikina haka nake jina
   Karya kike yi humaira kema kin sani nima na sani kin fada ne dan ki bata min rai ni kuma vazan damu ba dan nasan kina so na har zuciyar ki zan shanye koma menene zaki min nasan its obvious dama kiyi fushi dani dan ni me laifi ne a gunki kuma ban ga laifun ki ba dan zaki hukunta ni amma ki sani kiyi adalci a gun hukuncin naki horon ya min yawa kullum ni nasan yadda nake ji a jikna mutuwa nake slowly slowly a kan son ki duk abunda ya sameni ki sani kece sila kuma *a sanadin ki ne*
Ki.kuka da ksn ki ba da ni ba hakuri na ya kusa zuwa karshe zan miki komai dan na yi miki proving cewa ina son ki
  *humaira ni ke nake so*
Ya cikata ya fice waje a gun ta tsuguna tasa kuka irin kukan nsn with pain nims ina son ka hamma amma ya xama dole na nuna maka cewa ka min rashin adalci a baya nima ramawa nake yi amma na fika shiga wani hali domin san ka kullum karuwa yake yi a raina bai ragu ba koda sec daya ne balle yayi tangadi

For you my lovly sis
_ummu arif_
😘😘😘😘😘😘😘
[6:27PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*aisha humaira*
✨✨✨✨✨✨✨
*na*
*khairat up*
*57*

Washe gari data tashi daga barci ta wanke bakin ta tayi wanka ta daura zanin atampa ta gyara jikin ta dake ta tashi da ciwon mara
Dan ta girka abinci ta fita waje kawai ballons ta gani jajjaye shape din love da roses a kasan carpert din a kasa aka yi ado da flower me yellow ya rubuta
   *i love you Aisha humaira will you be mine*

Ya kulle mata ido ta baya
Me haka hamma ka rabu dani dole ne zaka dinga takura min
Shhhhh! Ya dora yatsan sa a kan lips din ta
Ya ja hannun ta zuwa cikin dakin sa
Kunce mata daurin yayi daga idan ta
Hotunan ta ta dinga gani ta ko ina manya manya window size an jera su a ko ina
 Bakin ta, ta bude cike da mamakin sa wai shin da gaske mutumin nan yake ?
Hamma waya maka wayanan abubuwan ?ka daina wahalar da kan ka ba su zasu sa na hakura na yafe maka ba ni na gama da babin ka
I just need space ka kyale ni all wayanan bazasu sa na damu da kai ba kamar da lokacin da na lallashe ka na nuna maka muhimancin ka a gareni ai baka yarda ba.shi yasa na ce maka kan ka kawai kake so.u re selfish wato kana nufin son ka shi ne so nawa was just rubbish? Hamma dan Allah ka daina wahalar da kan ka humaira bata sonka yanzu

Idan sa ya lumshe ya na kallon karamin bakin ta se zazzaga masa masifa take yi kawai ji yayi tsiwar ta ya burge shi

Ina magana hamma ksna kallona
Yes ke nake kllo saboda wani kyau kika kara da kina min wannsn tsiwar taki

Hmm!ok!to na gane me kake nufi na zama mahaukaciya ko?
    Hannun ta yaja cikin yan seconds ya mata abunda bata yi tsamani ba idanta kawai take blinking tana zare su dan kan sa ya cikata yana maida numfashi
  Da gudu ta fita waje
Shi kuma ksn gadon sa ya fada yana murmushi wayyo Allah na so da wuya yake kai jama'a dubi yadda na koma cikin kwana daya na zama mr.romantic harda aro tactics na malaman soyayya dan na samu ksn masoyiyata amma ta fiya taurin kai amma nima na iya taurin ksn zan lallabo ta

  Tana komawa dakin taga wata katuwar teddy ja da kuma wata yar karama rungume jikin teddy din an rubuta _i love u_
Humaira da teddy tayi smiling ta dau teddy din ta gyara masa zama ta kwanta kan gadon tana kallon saman cilin tana murmushi wow baxan manta wannan ranar ba tayi tsalle tana ihu da karfi da sauri ta toshe bakin ta au kar ya jini amma wannan hanyar dana bi ta hora hamma ita ce daidai am enjoying it alot

Gashi ta samu ganin other face na hamma masdook ya zama mr.lover din karfi da yaji abun ya burgeta flawers ,ballons,teddy,pictures abun kam ya mata dadi sossai kamar tace masa i love you to na yafe maka take ji amma bazata iya ba so take ta gama tantancewa da gaske ne yana son ta yanzu ko wani planning din sa ne again.

Lips dinta ta shafa yadda yayi laushi tayi smiling ta rungume teddy din i lyk it ta fada.

***

Kwanan shi hudu yana mata abubuwan mamaki da salo salo na soyayya wanda bata yi tunanin cewa ya iya su ba amma tayi biris da shi

Ransr na biyar ko ta dawo daga makaranta taga motar hamma yusuf a varander din waje da sauri ta karasa cikin gidan wani dadi taji ganin amira da fadima da hamma yusuf da hamma nas da hamma ni'imatullahi da hamma kamal
OMG!houseful gaba dayan ku kai amma.ina marhaba da zuwan ku
  Suka rungume juna ita da su fadima amma kun min baxata shi ne baku fada min nayi xamana ba a gida yau?

To da mun fada miki ya zamu ga wannsn expression din a face dinki?
 Wow wallahi naji dadin ganin ku sanunku ya hanya?
Alhamdulilahi ina kuka baro min dada ta?
  Dada na gida tana kewarki
Hawaye ya tarar mata a ido
 Allah sarki dada nima ina kewar ta nayi misin nata
   Tisssue ya mika mata mrs.cry amsa ke kuma kunzo zaku sa min mata kuka ko?
  Hamma nas yace lallai naga sauyi muda muka zo abin arziki shi ne za a mana kora da hali
Barshi hamma ai dan sun gan mu ne kar mu kashe musu jindadin kwana 2
  Au wai kwana zakuyi?
Ya fada da sauri
Aka sa dariya sossai humaira tayi kasa da kanta ta cusa ksnta jikn amira tana dariya kasa kasa
Gaskiya kuyi hakuri ku tattara ku koma gidan nas ni ina bukatar privacy da matata
   Hamma yusuf yace au Allah?
Eh mana!
To shi kensn tunda kace haka wallahi a nsn zamu kwana ke humaira jeki gyara mana dakuna guda uku na sama kin yi baki
   Wannsn ne kuma baka isa ba babu abunda zata yi kasa matar ka ta mska duk wanda ya matsu kuma yayi aure
Ni matata yar hutu ce
Ikon God
Se kallo inji hamma masdook
Ni'imatullahi yace aa meye zafi nikam zan bi nas mu tafi gidsn sa dan naga alama masdook baya son xaman mu a gidan sa kasan ango ne.

Ku dai kubi nas amma nikam.nan zan kwana sena rage masa jindadin kwana 2 nama fasa kwana dayan
Humaira dai tashi tayi ta shiga kichen dan masdook ya gama bada ita gun hamma yusuf
  Fridge ta bude ruwa ta dauko ta tsiyyaya a cup tana sha kawai ji tayi mutum ya riko kugunta ya hada da jikin sa yana shafa bayan ta  kiss ya mata a bayan ta lumshe idan ta tayi dan sakon ya isa gareta
Juyo da ita yayi ta yi maza ta kulle eyes dinta
  Pls ksr ki nuna musu we are not normal ki nuna masu komai ya daidaita a tsakanina dake dan Allah kar ki bani kunya i promise zan miki abubda kike so bayan sun tafi kinji amma ki bsni hadin kai yanzu mu kasance tare har se sun tafi mu dinga komsi kamar normal wife and husband duk da ni bani da matsala matsalar daga gunki take na baki hakuri kin ki ji na rasa mezan ce miki kuma humaira taurin kan ki yayi yawa.

  Hmm naji hamma amma ka cikani ba kowa a nan daga ni se kai seka bari se muna cikin su seka yi koma wane irin pretending ne amma banda yanzu i need freedom ban son kana taba ni haka wani.iri nake ji yadda kasan ana zuba min wuta a jikina haka nake jina
   Karya kike yi humaira kema kin sani nima na sani kin fada ne dan ki bata min rai ni kuma vazan damu ba dan nasan kina so na har zuciyar ki zan shanye koma menene zaki min nasan its obvious dama kiyi fushi dani dan ni me laifi ne a gunki kuma ban ga laifun ki ba dan zaki hukunta ni amma ki sani kiyi adalci a gun hukuncin naki horon ya min yawa kullum ni nasan yadda nake ji a jikna mutuwa nake slowly slowly a kan son ki duk abunda ya sameni ki sani kece sila kuma *a sanadin ki ne*
Ki.kuka da ksn ki ba da ni ba hakuri na ya kusa zuwa karshe zan miki komai dan na yi miki proving cewa ina son ki
  *humaira ni ke nake so*
Ya cikata ya fice waje a gun ta tsuguna tasa kuka irin kukan nsn with pain nims ina son ka hamma amma ya xama dole na nuna maka cewa ka min rashin adalci a baya nima ramawa nake yi amma na fika shiga wani hali domin san ka kullum karuwa yake yi a raina bai ragu ba koda sec daya ne balle yayi tangadi

For you my lovly sis
_ummu arif_
😘😘😘😘😘😘😘
[6:27PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
Aisha Humaira
✨✨✨✨✨✨✨
*na*
*khairat up*
*58*

Amira ta shigo.kitchen din kuma dama ta dadde jikin kofar da hamma zai fita seta buya a bsyan kofar tsugunawq tayi a kasa kusa da humaira
  Humaira rungume ta tayi tana kuka
Humaira naji komai amma abin yayi yawa ki daina wahalar da kan ki bayan kinsan komai kinsan cewa bszaki iya rayuwa ba tare da hamma ba then mesa kike wahalar da kan ki hamma da baya son ki amma yanzu ya dawo yana sonki seki sauko ku zauna lafiya
  Hmm amira kenan me kike nufi?
Ina nufin ki zauna da hamma lafiys ki manta da abunda ya faru a baya ki sauko ku zauna lfy.
    Ohh saboda yayan ki ne shi yasa zaki ce na manta wulakancin da ya min?
  Aa ba haka bane kar kiyi misunderstanding dina ba haka nake nufi ba naga kina wahala shi ma yana wahala kin fi kowa sanin hamma ...
   Hmm amira nagode amma ban gama yarda cewa hamma ya fara sona ba sena gama yarda tukuna kinsan dai ba wanda ya kain ni son hamma
 Na sani kowa ma ya sani
  So seki sa ido kiyi kallo kawai
To naji amma dan Allah ki sassauta masa horon yayi yawa 😜.

😃hmm zaki sani ai muje ni in huta
Kin ma isa muzo ki huta ai hira till down
Haba dea kin san ni dai zan iya barin komai amma banda abu biyu
 Na sani mana da bacci da kuma hamma yep muje to

***

 Tare suka yi girki su uku yan matan
  Suka jera a dinning suka zauna gaba dayan su abinci ne kala kala
  Hamma na gefen humaira amma ba abunda yake ci kawai juyawa yayi yana kallon humaira
 Nas ya tabo ni"imatullahi da kafa ya masa nuni da bakin sa alamar ya kalli masdook
Shi kuma ya tabo yusuf
 Suka fashe da dariya amma duk da haka baya jinsu be masan suna yi ba se humaira ce ta ji abun ya yi yawa ta dan harxuka wai me kuke dariya kamar wasu ...
  Amira tace ke kuwa ya ba za ayi dariya ba dubi hamma kamar an kafa shi a gun kin tafi da shi gaba daya in anyi magsna yace baya soyayya.

Juyswa tayi ta kalli hamma masdook kawai se ta ji kunya ta kamata sosaai ta take masa kafa
 Ouch!humaira,
Se suka fashe dariya ita kuma ta yi daki da gudu
Keyar sa ya sosa yana jin kunya kawai kun cika mana gida kun sa mana ido
  Au masoya mun kusa tafiya mu baku guri ni nasan ka matsu
 Wai shin wannan shi ne masdook kuwa wanda baya son humaira?
Ni'ima wallahi Allah ka kiyaye ni ina ruwan ka da bana so amma yanzu ina so se me?
Aa daga tuna maka baya se cibi ya zama 'kari.

Mikewa yayi ya koma dakin sa wanka yayi ya shirys tsaf se zuba kamshi yake yi ya koma kasa dakin humaira ya shiga tana zaune ta sake wanka amira ma na dakin kallon ta yayi ita kuma dariya take masa kasa kasa na tsokana hararta yayi yace out zsn gana da matata bsn san.gulma.
  Fita tayi tana tsoksnar sa gaskiya naga sabon hamma and am happy.
  Humaira zan wuce aiki
  Kallo ta bisa dashi aiki kuma?
Eh wani abu?
Baka gama warkewa bafa ka bari bayan kwana biyu ska koma
 Aa na huta da yawa kuma ina zaune ne ina tunani kala kala kwakwalwata zata buga tunda ke din ba kida tausayi so kike kiga na fadi na mutu tukuna seki yafewa gawata so better na fta akwai masu sona tunda humaira ta daina son hamma din ta
  Uhm'uhm se ka dawo
Allah yasa amin.

Taya zan nuna maka cewa na yafe maka am.testing you?
Nima sena rama yadda nima ka wahalar da zuciyata

Har ya fita ya dawo ya shigo dakin again yana kallon ta
Kukan me kike yi kuma humaira?
Ba komai
Ya zaki ce min ba komai ? Bayan ga hawaye kina yi ni na dame ki ko
Uhm
To yi shiru bazan kuma kinji yi hakuri share hawayen ki
  Hamma
Uhm ina jinki
Ya fada ya na cigaba da taya ta ninke kaysn nata
Hamma ina son ka bani izinin zuwa gida gun dada
Saboda me ?
Kawai akwai.amsoshin tambayoyi da nake nema daga gunta dan na kasa sukuni da hakura da hakan har sena ji ba'asi da kuma abunda kunnena yake son ji
 Ko zan iya jin me yake damun ki?
Hmm a baya na kwatanta hakan a da amma ban samu gamsasshiyar tarba daga gurin ka ba
Hmm maganar abban ki ce ko?

Uhm ita ce wadda a gurin ka bata da muhimmanci.

Ba haka bane humaira ban san mezan fada miki bane game da mahaifin ki saboda bazan iya fada miki komai ba amma ki shirya gobe se mu tafi tare katsinan kiji daga bakin baffa ko dada saboda na kasance d'aya daga cikin irin mahaifinki

Kallon sa tayi cikin mamaki
Hamma ban gane ba
Eh zaki gane nan gaba ni na kasance mara adalci , mara ksunarki ,mara bada umarni a gare ki amma ina neman afuwa a gareki dan Allah ki samu koda wata yar karamar kwana ce a cikin zuciyar ki na soyayya ki yafe min.

Wallahi tallshi ina sonki wannsn sabon masdook ne wancan masdook din ya mutu na fiso naga kina min kallon soyayya kina min kallon me adalci kina min kallon da kike min a da nayi missing din wannan looks din.

Humaira ya tsuguna a kasa

Ta mike da sauri subahanallahi hamma dan Allah ka mi'ke ka daina tsuguna min dan Allah kar ka sa min zunubi dan Allah ka tashi hamma ka tashi

Bazan tashi ba humaira ni na kasance me laifi a gareki na kuntata miki na bakanta miki na cuce ki na hanaki sakat na wulakanta ki....hannun ta tasa ta kulle masa baki kar ka karasa wallahi hamma tun tuni na manta da komai kawai ina dada tausasa zuciyata ne ina so in yarda da irin son da kake min.

Rungume ta yayi da tsauri nagode humaira nagode da kika yafe min tabbas kin kasance daya daga cikin mata masu yafiya masu hakuri da ladabi ga mazajen su
Humaira ina son ki

Mu yafi juna hamma ka fasa fitar?
Tun yaushe ai ni na samu gurin aiki ina zan iya fita  na barki ba
Kai hamma
Allsh kuwa
gaskiya ka zama lazy
Ai laifin ki ne
Ba wani dama can laxy ne
Baysn zuwanki rayuwata na zama lazyn
[6:27PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*aisha humaira*
✨✨✨✨✨✨✨
*na*
*khairat up*
*57*

Washe gari data tashi daga barci ta wanke bakin ta tayi wanka ta daura zanin atampa ta gyara jikin ta dake ta tashi da ciwon mara
Dan ta girka abinci ta fita waje kawai ballons ta gani jajjaye shape din love da roses a kasan carpert din a kasa aka yi ado da flower me yellow ya rubuta
   *i love you Aisha humaira will you be mine*

Ya kulle mata ido ta baya
Me haka hamma ka rabu dani dole ne zaka dinga takura min
Shhhhh! Ya dora yatsan sa a kan lips din ta
Ya ja hannun ta zuwa cikin dakin sa
Kunce mata daurin yayi daga idan ta
Hotunan ta ta dinga gani ta ko ina manya manya window size an jera su a ko ina
 Bakin ta, ta bude cike da mamakin sa wai shin da gaske mutumin nan yake ?
Hamma waya maka wayanan abubuwan ?ka daina wahalar da kan ka ba su zasu sa na hakura na yafe maka ba ni na gama da babin ka
I just need space ka kyale ni all wayanan bazasu sa na damu da kai ba kamar da lokacin da na lallashe ka na nuna maka muhimancin ka a gareni ai baka yarda ba.shi yasa na ce maka kan ka kawai kake so.u re selfish wato kana nufin son ka shi ne so nawa was just rubbish? Hamma dan Allah ka daina wahalar da kan ka humaira bata sonka yanzu

Idan sa ya lumshe ya na kallon karamin bakin ta se zazzaga masa masifa take yi kawai ji yayi tsiwar ta ya burge shi

Ina magana hamma ksna kallona
Yes ke nake kllo saboda wani kyau kika kara da kina min wannsn tsiwar taki

Hmm!ok!to na gane me kake nufi na zama mahaukaciya ko?
    Hannun ta yaja cikin yan seconds ya mata abunda bata yi tsamani ba idanta kawai take blinking tana zare su dan kan sa ya cikata yana maida numfashi
  Da gudu ta fita waje
Shi kuma ksn gadon sa ya fada yana murmushi wayyo Allah na so da wuya yake kai jama'a dubi yadda na koma cikin kwana daya na zama mr.romantic harda aro tactics na malaman soyayya dan na samu ksn masoyiyata amma ta fiya taurin kai amma nima na iya taurin ksn zan lallabo ta

  Tana komawa dakin taga wata katuwar teddy ja da kuma wata yar karama rungume jikin teddy din an rubuta _i love u_
Humaira da teddy tayi smiling ta dau teddy din ta gyara masa zama ta kwanta kan gadon tana kallon saman cilin tana murmushi wow baxan manta wannan ranar ba tayi tsalle tana ihu da karfi da sauri ta toshe bakin ta au kar ya jini amma wannan hanyar dana bi ta hora hamma ita ce daidai am enjoying it alot

Gashi ta samu ganin other face na hamma masdook ya zama mr.lover din karfi da yaji abun ya burgeta flawers ,ballons,teddy,pictures abun kam ya mata dadi sossai kamar tace masa i love you to na yafe maka take ji amma bazata iya ba so take ta gama tantancewa da gaske ne yana son ta yanzu ko wani planning din sa ne again.

Lips dinta ta shafa yadda yayi laushi tayi smiling ta rungume teddy din i lyk it ta fada.

***

Kwanan shi hudu yana mata abubuwan mamaki da salo salo na soyayya wanda bata yi tunanin cewa ya iya su ba amma tayi biris da shi

Ransr na biyar ko ta dawo daga makaranta taga motar hamma yusuf a varander din waje da sauri ta karasa cikin gidan wani dadi taji ganin amira da fadima da hamma yusuf da hamma nas da hamma ni'imatullahi da hamma kamal
OMG!houseful gaba dayan ku kai amma.ina marhaba da zuwan ku
  Suka rungume juna ita da su fadima amma kun min baxata shi ne baku fada min nayi xamana ba a gida yau?

To da mun fada miki ya zamu ga wannsn expression din a face dinki?
 Wow wallahi naji dadin ganin ku sanunku ya hanya?
Alhamdulilahi ina kuka baro min dada ta?
  Dada na gida tana kewarki
Hawaye ya tarar mata a ido
 Allah sarki dada nima ina kewar ta nayi misin nata
   Tisssue ya mika mata mrs.cry amsa ke kuma kunzo zaku sa min mata kuka ko?
  Hamma nas yace lallai naga sauyi muda muka zo abin arziki shi ne za a mana kora da hali
Barshi hamma ai dan sun gan mu ne kar mu kashe musu jindadin kwana 2
  Au wai kwana zakuyi?
Ya fada da sauri
Aka sa dariya sossai humaira tayi kasa da kanta ta cusa ksnta jikn amira tana dariya kasa kasa
Gaskiya kuyi hakuri ku tattara ku koma gidan nas ni ina bukatar privacy da matata
   Hamma yusuf yace au Allah?
Eh mana!
To shi kensn tunda kace haka wallahi a nsn zamu kwana ke humaira jeki gyara mana dakuna guda uku na sama kin yi baki
   Wannsn ne kuma baka isa ba babu abunda zata yi kasa matar ka ta mska duk wanda ya matsu kuma yayi aure
Ni matata yar hutu ce
Ikon God
Se kallo inji hamma masdook
Ni'imatullahi yace aa meye zafi nikam zan bi nas mu tafi gidsn sa dan naga alama masdook baya son xaman mu a gidan sa kasan ango ne.

Ku dai kubi nas amma nikam.nan zan kwana sena rage masa jindadin kwana 2 nama fasa kwana dayan
Humaira dai tashi tayi ta shiga kichen dan masdook ya gama bada ita gun hamma yusuf
  Fridge ta bude ruwa ta dauko ta tsiyyaya a cup tana sha kawai ji tayi mutum ya riko kugunta ya hada da jikin sa yana shafa bayan ta  kiss ya mata a bayan ta lumshe idan ta tayi dan sakon ya isa gareta
Juyo da ita yayi ta yi maza ta kulle eyes dinta
  Pls ksr ki nuna musu we are not normal ki nuna masu komai ya daidaita a tsakanina dake dan Allah kar ki bani kunya i promise zan miki abubda kike so bayan sun tafi kinji amma ki bsni hadin kai yanzu mu kasance tare har se sun tafi mu dinga komsi kamar normal wife and husband duk da ni bani da matsala matsalar daga gunki take na baki hakuri kin ki ji na rasa mezan ce miki kuma humaira taurin kan ki yayi yawa.

  Hmm naji hamma amma ka cikani ba kowa a nan daga ni se kai seka bari se muna cikin su seka yi koma wane irin pretending ne amma banda yanzu i need freedom ban son kana taba ni haka wani.iri nake ji yadda kasan ana zuba min wuta a jikina haka nake jina
   Karya kike yi humaira kema kin sani nima na sani kin fada ne dan ki bata min rai ni kuma vazan damu ba dan nasan kina so na har zuciyar ki zan shanye koma menene zaki min nasan its obvious dama kiyi fushi dani dan ni me laifi ne a gunki kuma ban ga laifun ki ba dan zaki hukunta ni amma ki sani kiyi adalci a gun hukuncin naki horon ya min yawa kullum ni nasan yadda nake ji a jikna mutuwa nake slowly slowly a kan son ki duk abunda ya sameni ki sani kece sila kuma *a sanadin ki ne*
Ki.kuka da ksn ki ba da ni ba hakuri na ya kusa zuwa karshe zan miki komai dan na yi miki proving cewa ina son ki
  *humaira ni ke nake so*
Ya cikata ya fice waje a gun ta tsuguna tasa kuka irin kukan nsn with pain nims ina son ka hamma amma ya xama dole na nuna maka cewa ka min rashin adalci a baya nima ramawa nake yi amma na fika shiga wani hali domin san ka kullum karuwa yake yi a raina bai ragu ba koda sec daya ne balle yayi tangadi

For you my lovly sis
_ummu arif_
😘😘😘😘😘😘😘
[6:27PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*Aisha humaira*
✨✨✨✨✨✨✨
*Na*
*Khairat up*
*52*


_ina mai baku hakuri kan rashin typing da wuri bana samun tym ne ina baku hakuri_

Bayan tafiyarta ya ga zaman bazai masa ba ya shiga ko zaiga abinci kan wani table dake cikin kicin din ya shiga ya buda tiffin din na saman kawai ba komai ciki na biyu kuma note ne a ciki ya buda yaga abunda ke ciki
    _hamma ka daina fushi da abinci in xaka yi kayi fushi da ni kadai ka cancanta ka nuna fushin ka gareni nasan bayan na tafi kana jin yunwa but bazaka tambayeni abinci ba saboda ego dinka amma na ajiye maka abincin saboda bsn son kana salalabawa cikin kicin da daddare kana daukar min abincina boye,pls kaci ka sha magani am not there but am there with u in my heart ko da kai baka sona ka sani ni ina son ka_

Murmushi ya kubuce masa ya dauko tiffin din da plate ya zuba abincin chips ne da kwai a cikin karamin flask kuma ruwan tea ne
Ya zsuna ya gama ci.
   Yana fitowa ya ga nas a falo xaune yana jiran sa mr.lover!
Hmm,wa kenan?badai ni ba ya nuna kan sa
Uhm muje nide a duba ka yau check up za a yi.

To muje .

***

Bayan sun gama ne ya ce ma nas muje ta makarantar yarinysr nsn mu dauko ta
 Ta gama lectures din ne?
I think so
Kirata dai muji dai kar muje she is not done.

Kiranta yayi lokacin suna aji suna daukar darasi na chem taji vibration daukowar da zata yi taga wake damun ta taga nun.
 *mr.arrogant*
Ta gwalalo idon ta waje cike da mamski a ranta tace look who is calling da sauri ta dauka ta kara a kunnen ta tana tsugunawa dan kar ta damu na kusa da ita
Hello ta fada ya jikin badai matsala ko ?
Ta tambsye shi a tare
Ya ce shhhhhh! kin gama lectures din ne?
Tayi jim sai kuma tace eh na gama
Owk ki jira ni gani nsn zuwa yau tare zamu tafi gida
 Hamma baka da lafiya fa wa ya ce kayi tuki kuma pls ka zauna a gida in kaji sauki seka fara tuki amma ur back is still.....kin fiya surutu tare da nas muke
Hmm ta fada tana ajiyar zuciya to sekun karaso.

Aisha humaira ko surutun tsiya bata bsri mutum ya gama maganar sa zata katse mutum da tambayoyi.

***
Kwatancan inda take ta masu a nsn nas yayi parking
Gogan yana daga cikin mota ya zugi tagar yana kallon wajan yadda mutane suka yi yawa a gurin musamman maza wani abu ya tsya masa a rai.
Mtsw .

A bakry ya tsaya yayo masu siyayya sannan ya sauke su a gida.



*53*

Be shiga ba ya barsu a nan ya koma gidan sa.

   Tsoron kama shi take yi kar ya mata tsawa jikin ta na rawa ta riko hannun sa kamar ze kwace se kuma ya barta ta taimaka masa ya riko ledar a hannun sa bude kofae tayi sannan ta shigar dashi.

Hamma zaka daki ko na barka a falo?
  Kmar me koyon magana yace barni a nan kunna min tv kisa min gun kwallo
Tom
Seme?
In anjima in ana da bukatsr wani abu zan kira ki amma tukuna bani ruwan lipton me dan citta a ciki.

A flask dan karami ta kawo masa ta ajiye
Da dan karamun cup to na taya ka kallon?
  Wani kallo ya mata aiko tasa dariya ta koma dakin kusa da falon ko zai kirata.

Murmushi yayi.kawai ya dauko cup din ya zuba tea din yana sha.
   Kallon champion league yake.

Har kusan karfe hudu yana kallon daga bisani ya mike yayi sallah sannan ya shiga dakin da take ta fito daga wanka kenan daure da towel ta yafa daya kan kafadar ta.
  Ganin an bude kofa yasa ta bi kofar da kallo duk da tasan waye amma bata yi tunanin cewa zai shigo ba din.

Kallo ya bita da shi sama zuwa kasa yadda lemar ruwa a jikinta
Lumshe idanta tayi zarazaran gashin idan ta ya kwanta a fuskarta
      Tsayuwa gagarar sa tayi kamar ya tsuguna a kasa haka yaji kawai ya saisaita ksn sa ki..hada..min...ruuuuwa...zan..yi...wankaaaa......

To ta fada murya na rawa
Ficewa yayi da bangon dakin ya jingina yana maida numfashin sa

Doguwar riga tasaka iyakarta cinya da sani pencil din wando pink rigar kuma yellow.

Ta daura pink din  dankwali ta fita dakin sa ta shiga ta hada masa ruwan ta zuba masa turare a ciki
Sannan ta sauka ta fada masa hamma na hada maka ruwan
To sannun ki
Muje man ki taimaka min na haw samsn ko bazaki iya ba?

  Aa zan iya mana in zaka yarda ai umarnin ka nake bi kai ka hanani kusantar ka kar na maka illah.

Hmm kin fadi gaskiya kin ce wani abu amma muje dai
Kugunta ya riko da karfi sossai yana jin kamshin jikin ta da kyar ta saisaita nutsuwarta ta taimaka masa ya shiga bandakin nasa kamshi ya doki hancin sa

  Besan sanda ya janyo ta ba jikin sa ya rungume ta tsam kamar za a kwace masa ita sumbatar ta ya fsra yi ksmsr wani mayunwacin zaki gaba daya bata da laka dan kan sa ya cikata ya hankada ta waje tangatanta tayi kamar ta fada kasa ta rike handle din kofar.
   Ta bisa da kallo kallon ka raina min hankali
 Shi kuma kallon amfanin ki kennsn a guna ya mata
Hawaye suka zubo mata a ce ayi rayuwa a haka.

Kofar ya banko da karfi ta ji abun har tsakar kanta
Lallai zan gyara maka zama ni bazsn dau wannan wulakancin ba ta share hawayen ta sannsn ta koma dakin ta.
[6:27PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨
*Na*
*Khairat up*
*59*

     _wannan page din naki ne my bestie fatima abubakar adam kina raina olwys Allah barmu tare amin 😘_

Wooo ni kuma,
Eh msna kina mamaki ne ?
Uhm'uhm kawai.dai ina nazari ne
Chakulkuli ya soma yi mata shaku ko shakku ko tana dariya tace aa wasa nake yi wasa nake yi dan Allah ka bari wallahi na tuba na daina
  Kima kara mana
Su nas na bakin kofa jin dariysr yayi.yawa yasa su leqowa gaba daya suna bakin kofar suka yi gyaran murya
Ehem ehem
 Humaira na kokarin kwacewa daga jikin sa ya dsda rike ta hamma ka cika ni suna kallon mu fa dan Allah ka cikani kaji

Kawai kun cika msna kunne kun manta cewa da wasu ma a gidan ba ku kadai bane 😏

To waya kawo ku? Dama ina neman hsnyar korar ku ina tunsnin yi muku kora da hali i think wannan shi ne best way na korar ku

Aa yi hakuri mana gobe xamu tattara mu koma mun gaji da wannan korar da halin da kake mana

Ato ku kuka sani
Wayar humaira ta soma ringing ta dauka taga sunan fatima a jiki da fara'a ta dauka
Hello ya kike?
Lafiya lou ya gida
Alhamdulilahi,kina ina ne?
   Ina gida
Haba koda naji dan na hahanga ban ganki ba
  Ta dafa goshin ta wai wallahi na manta fatima amma yanzu zan shigo makarantar
Ok sena karaso
Azo lafiya amin.

Kagani ko kasa na manta ina da lectures
Haba dan Allah gaskiya makarantar nsn zata uzura min ta shigar min rayuwata da yawa
Gaskiya kar kije nima kinga saboda ke naki zuwa.

Amma ni ai shhh yasa hannun sa a lips dinta ta nuna masa kofa ka manta su hamma nas na kofa

Kyalle su ganin kwakwaf ya kawo su kuma zan gyara musu zama kawai ki bani hadin kai kawai kin yarda nayi abunda nayi kinji.
Uhm ta fada ta gyada masa kanta.

Bakin sa ya kai kan bakin ta ita ksnta bata san cewa haka zai mata ba

Ihu suka sa daga waje suka yi falo da gudu shi kuma ya saketa yana dariya
Lah'ila hamma dubi me kayi ai shi kenan ka bsni kunya matsa min ta hankada shi ya fada kan gadon yana dariya

Yana tsaye ta canja kaya ta dauko mayafi yace aa mayar ai kin daina yar sa mayafi sede a gida ki min ado

Hamma ! Ba wani hamma da gaske nake miki ina tunanin ma zamu je kasuwa a dinko miki hijjabai kamar guda hamsin haka

👀👀 hamsin kuma?
  Yes
Amma why?
Cox am d boss!
Hmm mr.arrogant ni bsn sa hijab fa
To mrs.arrogant sekin sa
Amma bana so
Ni kuma ina so
Ta riko collar din rigarsa cizon sa tayi a kumatunsa zan sa amma yau kawai.

Uhm 🤔 zan yi tunani
Murmushi tayi kai mr.arrogant ka fiya kishi

  Matar tawa ce se ina kishin ta ya fada yana jan hancin ta muje na kai ki daga nan zan wuce aiki tunda ba kya nan

Wai mr.arrogant yaushe ka zamo mr.romantic
  Sanda na fara son ki hannun ta ya riko muje kar ki makara

Ina zaku lovers?
In da kuka aike mu
Oh humsira kin yarda masdook ya maida ke marar kunysr karfi da yaji ko ?
  Aa hamma makaranta zanje shi kuma seje aiki
To mu fa?
Kuyi gadin gidan inji hamma
To me mata se kun dawo to Allah sa ku msna girki fa
Hamma yusuf ya cilla masa fillow marar mutunci zan rama ne
Yo me ka iya kaida amiran taka ai de kasan na fika a komai a fannin lobbaya
Hehe wa yaga farin shiga basaban ba dama shi haka dan kauye yake da samun guri har yafi dan birni ma

Daga baya kenan
Se anjima kar kusa na makarar da.my love
To se kun dawo
[6:27PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
Aisha Humaira
✨✨✨✨✨✨✨
*na*
*khairat up*
*58*

Amira ta shigo.kitchen din kuma dama ta dadde jikin kofar da hamma zai fita seta buya a bsyan kofar tsugunawq tayi a kasa kusa da humaira
  Humaira rungume ta tayi tana kuka
Humaira naji komai amma abin yayi yawa ki daina wahalar da kan ki bayan kinsan komai kinsan cewa bszaki iya rayuwa ba tare da hamma ba then mesa kike wahalar da kan ki hamma da baya son ki amma yanzu ya dawo yana sonki seki sauko ku zauna lafiya
  Hmm amira kenan me kike nufi?
Ina nufin ki zauna da hamma lafiys ki manta da abunda ya faru a baya ki sauko ku zauna lfy.
    Ohh saboda yayan ki ne shi yasa zaki ce na manta wulakancin da ya min?
  Aa ba haka bane kar kiyi misunderstanding dina ba haka nake nufi ba naga kina wahala shi ma yana wahala kin fi kowa sanin hamma ...
   Hmm amira nagode amma ban gama yarda cewa hamma ya fara sona ba sena gama yarda tukuna kinsan dai ba wanda ya kain ni son hamma
 Na sani kowa ma ya sani
  So seki sa ido kiyi kallo kawai
To naji amma dan Allah ki sassauta masa horon yayi yawa 😜.

😃hmm zaki sani ai muje ni in huta
Kin ma isa muzo ki huta ai hira till down
Haba dea kin san ni dai zan iya barin komai amma banda abu biyu
 Na sani mana da bacci da kuma hamma yep muje to

***

 Tare suka yi girki su uku yan matan
  Suka jera a dinning suka zauna gaba dayan su abinci ne kala kala
  Hamma na gefen humaira amma ba abunda yake ci kawai juyawa yayi yana kallon humaira
 Nas ya tabo ni"imatullahi da kafa ya masa nuni da bakin sa alamar ya kalli masdook
Shi kuma ya tabo yusuf
 Suka fashe da dariya amma duk da haka baya jinsu be masan suna yi ba se humaira ce ta ji abun ya yi yawa ta dan harxuka wai me kuke dariya kamar wasu ...
  Amira tace ke kuwa ya ba za ayi dariya ba dubi hamma kamar an kafa shi a gun kin tafi da shi gaba daya in anyi magsna yace baya soyayya.

Juyswa tayi ta kalli hamma masdook kawai se ta ji kunya ta kamata sosaai ta take masa kafa
 Ouch!humaira,
Se suka fashe dariya ita kuma ta yi daki da gudu
Keyar sa ya sosa yana jin kunya kawai kun cika mana gida kun sa mana ido
  Au masoya mun kusa tafiya mu baku guri ni nasan ka matsu
 Wai shin wannan shi ne masdook kuwa wanda baya son humaira?
Ni'ima wallahi Allah ka kiyaye ni ina ruwan ka da bana so amma yanzu ina so se me?
Aa daga tuna maka baya se cibi ya zama 'kari.

Mikewa yayi ya koma dakin sa wanka yayi ya shirys tsaf se zuba kamshi yake yi ya koma kasa dakin humaira ya shiga tana zaune ta sake wanka amira ma na dakin kallon ta yayi ita kuma dariya take masa kasa kasa na tsokana hararta yayi yace out zsn gana da matata bsn san.gulma.
  Fita tayi tana tsoksnar sa gaskiya naga sabon hamma and am happy.
  Humaira zan wuce aiki
  Kallo ta bisa dashi aiki kuma?
Eh wani abu?
Baka gama warkewa bafa ka bari bayan kwana biyu ska koma
 Aa na huta da yawa kuma ina zaune ne ina tunani kala kala kwakwalwata zata buga tunda ke din ba kida tausayi so kike kiga na fadi na mutu tukuna seki yafewa gawata so better na fta akwai masu sona tunda humaira ta daina son hamma din ta
  Uhm'uhm se ka dawo
Allah yasa amin.

Taya zan nuna maka cewa na yafe maka am.testing you?
Nima sena rama yadda nima ka wahalar da zuciyata

Har ya fita ya dawo ya shigo dakin again yana kallon ta
Kukan me kike yi kuma humaira?
Ba komai
Ya zaki ce min ba komai ? Bayan ga hawaye kina yi ni na dame ki ko
Uhm
To yi shiru bazan kuma kinji yi hakuri share hawayen ki
  Hamma
Uhm ina jinki
Ya fada ya na cigaba da taya ta ninke kaysn nata
Hamma ina son ka bani izinin zuwa gida gun dada
Saboda me ?
Kawai akwai.amsoshin tambayoyi da nake nema daga gunta dan na kasa sukuni da hakura da hakan har sena ji ba'asi da kuma abunda kunnena yake son ji
 Ko zan iya jin me yake damun ki?
Hmm a baya na kwatanta hakan a da amma ban samu gamsasshiyar tarba daga gurin ka ba
Hmm maganar abban ki ce ko?

Uhm ita ce wadda a gurin ka bata da muhimmanci.

Ba haka bane humaira ban san mezan fada miki bane game da mahaifin ki saboda bazan iya fada miki komai ba amma ki shirya gobe se mu tafi tare katsinan kiji daga bakin baffa ko dada saboda na kasance d'aya daga cikin irin mahaifinki

Kallon sa tayi cikin mamaki
Hamma ban gane ba
Eh zaki gane nan gaba ni na kasance mara adalci , mara ksunarki ,mara bada umarni a gare ki amma ina neman afuwa a gareki dan Allah ki samu koda wata yar karamar kwana ce a cikin zuciyar ki na soyayya ki yafe min.

Wallahi tallshi ina sonki wannsn sabon masdook ne wancan masdook din ya mutu na fiso naga kina min kallon soyayya kina min kallon me adalci kina min kallon da kike min a da nayi missing din wannan looks din.

Humaira ya tsuguna a kasa

Ta mike da sauri subahanallahi hamma dan Allah ka mi'ke ka daina tsuguna min dan Allah kar ka sa min zunubi dan Allah ka tashi hamma ka tashi

Bazan tashi ba humaira ni na kasance me laifi a gareki na kuntata miki na bakanta miki na cuce ki na hanaki sakat na wulakanta ki....hannun ta tasa ta kulle masa baki kar ka karasa wallahi hamma tun tuni na manta da komai kawai ina dada tausasa zuciyata ne ina so in yarda da irin son da kake min.

Rungume ta yayi da tsauri nagode humaira nagode da kika yafe min tabbas kin kasance daya daga cikin mata masu yafiya masu hakuri da ladabi ga mazajen su
Humaira ina son ki

Mu yafi juna hamma ka fasa fitar?
Tun yaushe ai ni na samu gurin aiki ina zan iya fita  na barki ba
Kai hamma
Allsh kuwa
gaskiya ka zama lazy
Ai laifin ki ne
Ba wani dama can laxy ne
Baysn zuwanki rayuwata na zama lazyn
[6:27PM, 3/14/2017] Kairat Up: [22:45, 19/02/2017] Ummulkhair.S.Panisau: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨
*na*
*khairat up*
*60*

  _bayan kwana biyu_

*katsina(dikko)*

Dada ta rungume ta tayi tsam tana kuka
   Ke yar nan me na kuka?
Kewar ki mana dada na yi kewar ki da yawa   Allah sarki jikalle nima ina ta tunsnin ki kina csn kina hutawa abunki kin msnta da wata dada can.
  Tab di baki san yadda na yi kewar ki ba
 To ya gidan ?
Lafiya lou
   Amma dai ba damuwa ko?
Eh komai lafiya lou
To masha Allah
  Bara naje gun su inono mu gaisa sannan na je gun mama zan dawo ina da magana da ke fa me kyau.
  To se kin dawo
Allah sa
Amin!!

Bayan ta gaisa da ko wannen su ta dan dadde
  Tana fitowa taji an jawota jikin kofa ya hadeta ya mata katanga da hannayen sa
 Ta dora hannun ta a kan kafadar sa tana jan hancin sa da daya hannun nata mr.arrogant ka fiya shakiyanci.
  Uhm mrs.arrogant ke kika sani zama shakiyayen ai
Oh really!
Yep yanzu da haka zaki tafi baki neme ni ba kin shigo gidan namu?
To afwan amma dea kasan dalilin zuwan nawa ko?
Nasani amma be zama cewa ki.ki bani time ba ko?
  Haka ne amma so nake ayi ta ta kare  gaba daya.
Haka ne muje na raka ki!
Uhm'uhm ku gama ganawa da mama tukuna
 Aa muje ai mama bata da matsala xata gane cewa masdook yana da bukatar matar sa a kusa.
 Kai kam.ka xama mara kunya laifin ki ne matas.
  Kasan me?
Aa ya fada yana jawo hannun ta muje ina jinki
  Kawai ina mamakin yadda muka zama daya cikin kankanin lokaci
Dama can daya muke kawai ban gane da wuri ba se yanxu kuma ki daina mamaki da ikon Allah komai me faruwa ne
 Haka ne tare suka shiga cikin gidan suna hira kasa kasa kawai sede kaji dariyar su ta masoya cikin shaukin juna da son juna kamar wasu *(romeo & juliet.)*

Dada ta
Ba wani nan ja'iri tunda ka dau matar ka kuka bar garin nsn ban kuma ganin ku ba zaka min wani dadin bakin ku na maza
  Dariya yayi to ya za ayi tunda nsyi amarya ai dole na bar uwargida tunda ta tsupha
  Hehe lallai da me ta fini zamanancin ko barbada kumatu??
Abun dariya ya basu suka sa dariya gaba dayan su harda kuka humaira
Ni na isa nafi uwargida kyau ?
Ato kema ai kin sani shi yasa
Sossai ma dada
Kai hamma ka daina tabo min dada kaji ko
Yasa hannu shi a goshi alamar yana saluting dinta yes ma!
Kinji ko ya daina
 Rasa yadda zata yi ta tambayi dada maganar abban ta take saboda bata taba yi mata ba
  Dada
Uhm ina jinki
Dada waye abbana?
*ni yar waye*?

Kallon ta dada tayi tana mamskin ta humaira mesa kika tambaye ni wannan maganar yau cikin shekarun da suka wuce baki taba tunkarata da wannan maganar ba se yanxu?

Dada wallahi kusan kullum kwana biyu tun bayan komawata kano naji duk duniya ba abunda nake son gani kamar mahaifina dada koda sunan sa ne ki fada min zan iya hakura da ganin fuskar sa ma

Hmm!gaskiya ne humaira ni dama nasan hakan xata faru duk daran daddewa zaki min wannsn tambayar ko ba dadde ko ba jima na san da hakan amma ina tsoron wannan ranar tazo saboda bana son na rasa ki duk da nasan ban yi laifi ba amma bazsn hanaki sanin ainihin mahaifinki ba.

Dada waye mahaifin *aisha humaira**?*
 Mahaifin aisha humaira sannan ne a garin gombe

To dada waye shi?
Mutumin kirki ne mutum ne me nagarta mutum ne me hakuri sede kunsan ance mutum baya wuce kaddarar sa duk abunda Allah yaso to seya faru komai kaga bawa yayi to daga Allah ne kuma rubuttace ne.

Haka ne dada
Kar ki rike mahaifin ki humaira dan abunda ya faru illa ki dauke ta a matsayin kaddarar ki kawai abunda ya bata min rai yasa na dauke ki daga hannun su saboda ina tsoron kar a min sanadin ki ksmar yadda yayi sanadin mahaifiyarki saboda sakacin su.

Dada sakaci kuma?
Eh masdook sakaci kuma mugunta da rashin kulawa

To dada muna jinki ki fada mana man.

Ka kirawo min baffan ku da yusuf da ni'ima da dai sauran yan gidan kowa yaji komai mahaifin humaira nada rai .
  To dada
Jikin humaira dai yayi sanyi sossea kawai ta kosa taji me ya faru a baya kardai ace *baya da kura*

   Kamar yadda dada ta fada haka masdook yayi ya kirawo duk wayanda ta bukata ya kirawo su.

To duk dai kuna nan ko?
Eh dada duk muna nan muna sauraron karin bayani daga wajan ki
To to alhamdulilahi

*ASALIN LABARIN*
          *DA*
*KUMA*
          *DANGANTAKAR DADA DA IYAYEN MASDOOK*
[20:28, 20/02/2017] Ummulkhair.S.Panisau: 61

Malam.mubarak umar dikko mijina kenan ni khadija ibrahim dikko matar sa guda daya jal yana da amini wato mahaifin muhammad (maihaifin masdook).
  Aminsa mal.idris kabiru dikko
Sun taso tare tun suna yara har girman su kunsan fulani da yawo gari gari da canjs guri to haka take a gun su mijina da mahaifin muhammad.
Aminai ne na sossai wanda har suka yi ginin wannsn gidan guda biyu iri daya kasancewar idris maraya bashin da kowa iyayen sa su kadai suka zo garin nsn na katsina se Allah ya yi musu rasuwa dalilin wata gobara da akayi a rigar su can wani daji se mahaifin mijna ya rike shi dake shi kadai suke da
Hakan be hana malam rike su ba .
  Ba wani.ilimin boko suka yi ba illa sun yi ilimin muhammadiya komai tare ake musu har girman su se ya kasane duk wani sani a harkar gona Allsh ya musu sani a nan basu da matsala

Bayan bikina da mal.da kuma bikin idris da mama ba karamin jindadi iyayen su ka yi ba murna sossea gida daya muke a hade da ni da mama matar idiris

  Cikin shekara da rabi muka haihu tare nida mama muka haifo maza na samu idris wanda yaci sunan abokin malam wato(baffa idi kennan)

Ita kuma ta samu muhammad daga nan Allah be kuma bata haihuwa ba saboda cikin ta na biyu ta fdo daga saman bene se ta samu matsala tun daga nan bata kuma samun rabo ba.

Ni kuma bayan idris na samu ibrahim,sadeeq da kuma aisha humaira yar'auta ta

Duk gadon iyayen su suka yo wato noma kensn sede sadeeq da ya nemi yin karatu shi da muhammad aka tura su birni su biyu.

Aisha kuma mafi soyuwa guna da kowa ma saboda fara'ar ta da son mutane ga nutsuwa da ilimi
Sossai ina son aisha

Sadeeq da muhammad cikin shekaru bakwai suka kammala karatun su suka dawo lokacin ko aka yi bikin su gaba daysn su maxan dake mu ba a daddewa ake yi ma maza aure matukar suna da sana'ar su

Se aisha dake cikin shekaru goma sha daya a duniya kanwata marayama tazo daga gombe inda take aure a kumo tazo gaida ni tace na bata aisha.hutu da kyar muka yarda musamman malam da baya son dan shi yayi nisa dashi.

A can maryama tasa humaira a makarantar pri ta fara daga farko a gidan da akwai kanin mijin ta dake mijin nata yana aikin asibiti ne a can kumo din.

Wasa wasa har aisha ya zamo tayi sabo da su a can sossai shekarata daya malam ya aika daukota nan fa sunusi ya lallaba su idiris ya musi bayanin dalilin rike aisha su Allah be basu haihuwa ba
  To zamu fadawa abba batun ka amma tukuna dai kasan shi me yake so?
Aa
Shi yafi son tayi aure tukuna
  Nayi masa alkawari zsn aurar da aisha zan mata gata irin wadda ya kamata ko wane uba yayi wa diyarsa ta cikinsa amma da zarar ta gama makaranta gaba daya dan tayi nisa a karatun ta.

To za kaji daga bakin abban in mun koma
To ke aisha kin zama yar gombe ko inna daga aro kin rike mana kanwa
  To ya za ayi ku kuna da yawa gun yaya amma ai ba kamar humaira ba dan kun daukewa dada zuciyarta gaba daya da kyar take sukuni saboda rashin humaira kusa da ita.
 Ayya ai zata zo htu
Hhh lallsi.muma ma riketa daga hutu a hsba dai nasan cewa yaya beze hana min rikon humaira ba insha Allah
To Allah ya yarda amin.

Kwansu biyu suka koma masa da bayanin sunusi ya gyada kan sa yace shi kenan baxsn iya hana maryama aisha ba amma zan samu lokaci nida idrisa muje can garin mu gansu na ganta dan ina kewarta sossai
 To abba ina jin ma mama da sadeeq zasu je da matar sadeeq
To ai shi kennan wani satin se muje can garin
 Allah ya kaimu amin.

Wannan ranar da suka yi tafiys ta kasance bakar rana a garem gaba daya suka shirya suka yi hsnyar gombe a lokacin dada bata da lafiya tana fama da ciwon asthma .

Kwaan su daya abba ya ce ma sunusi ya bashi amanar humaira kuma ya bashi ita har abada ya riketa da kyau tamkar wasiya ya bashi kana da ikon bawa wanda kake so auran humaira amma me addini da tsoron Allah domin aisha humaira rayuwata ce ina mutukar kaunarta domin kuwa ina baka rayuwata ne saboda haka ka riketa da kyau
Insha Allah hamma na rike.
 Ke kuma maryama aisha ta zama ysrki ke kike da iko da ita saboda haka gata nan

Humaira ko ba a fada miki ba ki sani wannan sun zama ginshiki a gareki kuma iyayen ki banda rashin kunya bsnda rashin kirki in kin musu tamkar mu kika yiwa ki rike tarbiysr mu kuma kiyi abunda suke so ki kasance me hakuri da juriya a garesu
Insha Allah abba zan yi duk yadda kace
To alhamdulilahi idris kana da abun cewa ne
Aa ai ka gama fadar komai mubarak
To masha Allah muje ko
Hamma sadeeq ga wannan a kaiwa ni'imatullahi
Aa shi kadai?
Kasan shi ne na wurina
Lallai.kinyi kuskure ai masdook ma kinsan yana ji dake kullum aunty
  Dariya tayi to a basu dukkan su yaran hudu to humaira mu zamu wuce aa da wuri haka
Ke kuwa kwanan mu biyu fa
Allah ya kiyaye hanya amin.
[6:27PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*Aisha Humaira*
✨✨✨✨✨✨✨
*na*
*khairat up*
*66*

   Kwance take jikin masdook tana zubda hawayen ta yana jin sa ransa a duk a dagule yake jin hawayen humairarsa na xuba gashi bashi da yadda zai yi yasa tayi shiru ko ya hadata da mahaifin ta saboda dada da alkawarin da ta yi ma mahaifiyar ta.
Mikewa tayi da sauri hamma yanzu shi kenan bazan ga dan'uwa na ba wanda muke ciki daya dashi?
     Kiyi shiru humaira ki daina kuka dan Allah ki bari kinji nima so kike nayi kukan nima
  Aa!hamma kawai ina kukan wahalar da mamana ta sha da rashin yardar da mahaifina ya nuna a gareta yanzu haka maza suke yi.idan suna da mata biyu se daya ta zamo bora daya kuma mowa?
   
   Shhh ba haka bane kinsan kowa da halin sa kuma in kin duba abinda ya faru duk rashin fahimta ne da makirci na mata mahaifin ki bashi da laifi sossai a lokacin ko nine aka fada min cewa kinyi wa mama haka bazan saurari komai ba zan dau hukunci a kan ki dan kuwa uwa ta fi kowa.
   Bare .....hamma yanzu bayan sa zaka bi saboda kaima namiji ne?
  No! Ba haka bane ina nuna miki ne
 Ni ba abunda xanji ai dama nasan kana son ka karo.aure ko ka auri tsohuwar budurwar ka zainab dan nasan har yanzu tana bibiyar ka bata barka ba kuma....hannun sa yasa kan lebbun ta aisha humaira ki daina min magansr ta domin kuwa zainab past dina ce ke kuma present dina na riga da na msnta da ita bana son zainab tun lokacin da ta ki mutunta dangina da kuma mutunta su tun ranar nayi watsi da ita na shafe babin ta a rayuwata ki dsina tunanin zan auro miki ita sam ba haka bane
    Ta mike tayi waje fuu
  Kan sa ya ksma yace
*women i tell u*
*Wuyar sha'ani!*.

Dakin mama ta koma ta kwanta a kan gadon ta se hawaye ne suke zuba mata wani irin haushin maza ma take ji gaba daya

Mama humaira ta shigo nsn ne?
 Eh tana dakina naga ta shigo tana kuka
  Amma baki bita ba mama
 Baba humaira nasan tana bukatar tayi kukan a halin da take ciki yanzu
Amma mama?
Hannun ta ta daga masa ya isa baba kaje ka huta ka barta ta huta tayi kukan ko ta ji sanyi a ranta!

Mama ya xan iya barin ta tayi ta kuka
To se ka yi ai kaje din

Zaunawa yayi a kan kujera kusa da ita yana rike da kan sa
Mama wai mesa mata basa da zurfafa tunani kin san ko humaira nima tana min kallon abunda mahaifin ta ya ma aunty nima zsn mata saboda zainab
Ina tunanin zainab dun kun rabu?
Eh mama ni na rabu da ita amma ita har ynzu tana nema na a waya
  Kai ka jiyo soko kawai kai ka jiyo
mama nifa bana kulata wallahi ban san yadda akai humaira tasan ta ba
 Baba ka tashi kayi wanka ka tafi massalaci kar ka cika min kunne da surutu

Ficewa yayi dakin sa ya koma direct wanka yayi ya fito ya shirya cikin kaftan ya sa turare ya daura agogo sannan ya sa takalmin sa hular sa ya saka a kan sa ya shiga gun mama tana falo har a lokacin amma kallo take
  Mama xan wuce
To a dawo lafiya
Amin.
 _ni zan wuce massalaci ina fata ki huce kafin na dawo dan in ba haka ba zan shigo har dakin mama na lallaba ki with my own style seki zaba na lallaba ki cikin gidan surukai ko kuwa?_
        _MMD_
Yq fice yana murmushi
Tana jin shigowar sakon ta duba ta karanta tana daga kwance lokacin ta karanta tsaki tayi hade da smiling ta tura masa in short
_ni ba ruwana da kai ba ma seka san inda nake ba harda tura masa harara_
      _AMD_
Yana mota yusuf ke tukin ya ga sakon murmusawa yayi yana shafa sajen sa
 Yadai man?inji nas
Idon matambayi
Maida wukar
 _akwai inda ruhina zai shiga na kasa nemo shi ne?mrs.MMD?_

Ta fito daga alwala ta ga sakon dariya ya ba sossai wai ruhin sa

_ruhin ka ai sede zainab me ruwan aisha humaira 😏_
      _aisha humaira_

Hmm ya ajiye wayar a aljihun sa saura se hira suke yi a tsakanin su amma gogan ya tafi wata duniyar ta tunanin masoyiyarsa
  Wayaga fushin masoyi hutu .

***
Wasa wasa har dare bega humaira ba kuma mama ta hana shi tsallake fallon balle ya shiga dakin nata kan dole ya zauna a falon
_haba my humaira hukuncin ya min tsauri da yawa ki fito koda fuskar ki ce na gani msma ta kafa ta tsare na ganki kema kin bada gudunmowa me kike so nayi ki yarda cewa na rabu da zainab tun kan nasan zan fara soyayya dake ki tausayawa bawan Allahn nan me son ki da gaskiya_

Sallah ta idar taga sakon nasa se kuma tausayn sa ya kamata
Dankwalinta ta daura ta fice falon bakin ta a zumbure
 Nesa dashi ta zsuna tana kumbure kumburen fuska
  Ya msnta ma a falon msma suke da sauri ya je ya rungumeta tsam ksr ki.kums nesanta kan ki daga gareni humaira *it hurt's*

Hamma me haka mama fa na kallon mu!
  Barta ta kalle mu seta kuma yarda da yadda nake kaunar ki na ke son ki gobe bazata kuma hanani ganin ki ba gwara tasan aisha ta maida masdook majnoon

Lallai baba to ja matar ka ku tafi can ku ksrats ni dama ina ruwana ai yar kallo ce ni
  Kin ji ko korar mu take ya ja hannun ta tana mutsu mutsun kwacewa amma ya mata rikon tsauri haka suka fita daga bangaren mama dakin sa ya nufa da ita ya kullo kofsr dakin kan kujera ya dora ta yw tsuguna shi kuma kallon ta yake yi kswai can tace hamma mesa kake min wannsn kallon?
 Kawai ina kallon iko na Allah daya bani ke matsayin mata ta ta sunnah me hankali da nutsuwa ni nasan matata is *brave* kuma ina son ki daina damun ksn ki insha Allah zaki ga mahaifin ki da danuwan ki da nayi.tunanin zuwa cam garin na taho dasu sede dada ta hana amma zan yi tracking nasu se...
  Aa kar kayi lets respect dada's emotion zsn hakura har se ya kawo kan sa inda nake ya neme ni ina son amsoshin tambayoyin da suka taru a zuciyata
    Uhm as u wish ma lady!
Amma xan miki warning kar ki kuma boye min ksn ki ko ki guje ni in ba haka ba ya ja kunnen ta
 Am.sorry my _MMD_
to tell me nine wa?
 🤔uhmmm
Ya dunkule hannun sa kamar wanda yake shirin yin dambe seta yi kissing din hannun nasa tace nice
*Aisha humaira matar masdook dikko his only mata my only miji*

Dariya yayi ya rungumeta ita ma ta rungumesa love u suka fada a tare!
[6:27PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*Aisha humaira*
✨✨✨✨✨✨✨
*na*
*khairat up*
*63*

Hanyar su ta dawowa birkin su ya lalace kuma ga wata mota na zuwa katuwar mota sunyi kokarin kaucewa amma Allah be nufa ba tayi out da yan motan babu wanda ya shura a cikin su gaba daya yan cikin motar malam,idris,sadeeq,mama,yafindo,du basu yi rai ba haka aka kawo mana gawar su gida ba karamin gigita aisha tayi ba har aka yi arba'in suna garin katsina.

Watan ta biyu garin ta koma saboda makaranta se ya xamana komsi na gidsn ya koma hannun dada ds baffa idi domin kuwa ysnxu sune manya shi da abbi se ibrahim dake binsu.sun tsaya tsayin daka wajan ganin komai na gidan su na tafiya daidai babu wani gargada ko takura sun yi kokari wajan basu tarbiya da kuma basu ilimin islsma babu takura in ksna son boko za a saka in baka so baza a saka ba ya rage naka Allah ya azurta familyn dada da yara maza duk da basu da wani yswa sossai cam.amma alhamdulilahi sun godewa Allah ko wannen su yana girmama na gaba dashi a familyn har sha'awa suke bawa mutane ga harkokin nomam su alhamdulilahi ana samu ba laifi.

Baffa idi yaran shi biyar tun kafin mutuwar malam
Isyaka,yusuf,nasir,fadimatu da rabi'atu.

Baffa iro kuma nada hudu shi kam duk mata se namiji daya
Asiya,firdausi,asma'u da kamal.
Shi dama baffa sadeeq kwansa daya a duniya kamin rasuwar sa shi ds mstar sa ni'imatullahi wanda dada ta raine shi tare da inono wato matar baffa idi.


Se muhammad (abbi)da ke da guda biyu rak
Masdook da kuma zainab (amira)

*gombe*

Humira na gama sakandare kanin mijin sunusi ya aureta amma yana da mata kuma gidan sa ya gina ya dauko mahaifiyar sa da kuma uwargidan sa mardiya wadda bsta kaunar aisha ko kadan shi kuma ahmad ba abunda Allah ya dora masa son sa kamar aisha tun kafin ya auro aisha komai zeyi zece aisha komai zai yi zai ce aisha komai ita hakan ba karamin bakantawa mardiya rai yake ba seta dau wa ksnta alkawrin ba abunda ahmad zai ki nsn gaba kamar aisha .

Farko farko ta nuna tana son aisha dan ta nunawa mijinta its daga gurin ta ba za a samu matsala ba dan ya ysrda da ita haka ma gwagwon sa.

Shi me yawan
 tafiye tafiye ne sabida harkar kasuwancin sa ba garin da baya zuwa yana kawo musu kaya komai iri daya
   Se kwanan aisha zata fara cutsr.karys aisha bata cewa komai don hakuri gareta
Ran girki kuma abincin ta kamar  ta roka haka ake bata shi amma bsta magana ranar da gwagwon ta tayi magana ranar mardiya ta kisisine fuska haba gwagwo me kike nufi ina cutar yarinyar nan?
Ke aisha kiji tsoron Allsh kefa kika ce abincin nan ya isheki kuma seki kawo karats gun gwagwo saboda bakin hali ta fashe da kukan karya
  Ni aisha bsta fada min komai ba nina lurs da hakan ki dai dinga jin tsoron Allah dan duniyar nawa take?

Gwagwo salamu alaikum
  Gwagwo meya faru ?
Aa mardiya lafiya kike kuka?
  Ka tambayi gwagwon ka mana duk nan nan da nake da matar ka ina lallabata naga yarinya ce amma gwagwo bata gani ita matar ka munafuka ce seta dunga fadawa gwogwo karya a kaina ita kuma gwagwo seta yarda da haksn kullum in na zuba mata abinci sta ce kadan shi ne xata hadani ds gwagwo
   Ke aisha bana son fitina fa kina ji ko ita ba yayarki bace mena ki na fadawa gwogwo salon hada fitina
  Budar bakin ta cewa tayi yays kiyi hakuri bazan kuma ba
  Shi kenan ni dama kin san ban dauke ki kishiya ba se kanwa ki daina halin ki mu zauna lafiya
 To
Ki bani ruwa na sha dan na gaji daga ganin ka ai kam.
  Ina ga gwagwo kawsi ko wacce ta dinga girkin ta haksn ma yafi ahmadu haksn yayi
  Haba dea a raba girki ki bari zan dinga yi ni ba damuwa ko har yanzu kina ganin ina kwarar ta ne ?

 Gwagwo ba komai fa ta dinga yi ba matsala
Kin tabbata aisha eh
To shi kenan ai.

***
Ai kindinga ganin masifa kala kala ba boka ba malam se kisisina mara mutunci kawai ki kwacan miji kina wani simi simi da iyayi kamar munafuka zaki yi bayani .

Cikin wata biyar ta samu juna biyu hankalin mardiya ya tashi lokacin mijin yana umara shi da gwagwo ta dinga hada mata shirme wai magani a haka cikin ya salwanta ya lalace tayi bari

Shekarar ta uku a gidan daga a sace mata kaya ko a dauke wari da wari a bar wani ko a dauke takalmi ko dan kunne ko sarkar ta amma bata taba yin magana ba ko ta nuna hakan
Mardiya kuma ta haifi namiji umar faruk
A lokacin ciki ne da aisha amma ita ma bata sani ba seda ya fito lokacin ba yadda mardiya xatayi ba karamin dadi gwagwo da ahmad suka ji ba da wannan rabon.

Haka ta haifi namiji abu ya tsaya mata a rai bakin ciki kamar me ai seta hada tuggu aisha na wanka kuma yan barka basu fara zuwa ba ta shiga dakin ta kira gwagwo daga dakin wai taje ta huta zata kula da yaron bata kawo komai ba ta koma dakin ta
 
   Ashe allurai ne a hannun ta kusan guda hudu ta bude bakin yaron ta zuba masa su a bakin sa .
 Ta koma waje
 Aa mardiya ya kuma naga kin fito?
Eh zan duba faruk ne
To bara naje ni

Tana shiga taji ysron nata kuka aisha ta fito kenan sega gwagwo seta ki daukar yaron se gwagwo ta dauke shi rarrashin duniya yaki yin shiru se kuka yake yi ksmar ransa ze fita ke aisha bashi mama muga ko zsi kama?
Uhm
Ungo shi ta amshe shi gwagwo kinga jini ke fitowa daga bakin sa
Jini?
Eh jini
Aa subahanallahi kirawo ahmad a waya yaxo maza maxa a kai shi asibiti a duba shi

Baban faruk ka zo da sauri yaron nan bashi da lafiya
  Aah bashi da lafiya meya same shi
Jini ke fits ta bakin sa haksn nan
Innalillahi wa inna illahir rajun gani nsn zuwa

  Mardiya ta shigo yana ji yaron nsn na kuka haka ins aisha din ne?
 Subahanalahi yana ga haka?
Ta amshe shi zuciyrta fal murna dadi take ji sossea.

Be wani dade ba ya dawo gida asibiti direct ya wuce da yaron likita ya duba shi ya kwantar dashi a kan gado don ya duba shi

 Ya gano allurai ne kuma sun huhuda shi a makogwaro gurin ya kumbura sosssi shi yasa jini ke fitowa ya masa allura ya samu ya kwanta
  Bayani yayi wa ahmad kan abunda ya gani kokarin kashe yaron aka yi
 What!
Allurai a cikin bakin sa garin yaya
To dai gashi nsn aiki za a masa a ciro masa su kuma se an kai shi babban asibiti tukuna likita kafin nan ai yaron ya jigwta ka taimaka kayi masa ni ba surgeon bane wannsn aikin se surgeon amma bani ba
[6:27PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨
*na*
*khairat up*
*69*
*_daga fadar_*:-

*©* *hikima writers assosiation*

Da sauri ta matsa kusa dashi ta riko hannun sa ta shafa fuskar sa ta taba hancin sa da kuma kafadar sa sai ta juya ta kalli faruk ma ta taba shi ta juyo ta kalli masdook
 Kai ya gyada mata alamar da gaske ne yan'uwan ta ne

Rungume me sunan malam tayi tana kuka ta fashe da kuka mara misaltuwa na cika burina yau naji dadi nagodewa Allah yau gani ga yanuwana dada yan'uwana ne da gaske ta rungume shi sossai

Ya dagota ki daina kuka dan Allah ki daina ki barni na ga kanwata da kyau na kalli kwayar idan ki naga kammanina dake naga kamanin ummi na a tare da ke naga halayan ta da suke tare da ke wallahi nayi kewar ki yar'uwata kullum da tunanin ki nake tashi

Ya faruk ga aishan mu nsn me sunan ummi na ina ma ina da rabon da zan kuma ganin ta ina ma ina da rabon dazan rungumeta na kira ta da *ummi*
   Sede ban da wannan rabon haka Allah ya tsara mana tamu kaddarar kuma na yarda da ita
   Aisha ki manta da komai kinji mu yayyan ki ne
 Haka ne ni dama ban rike ku ba kawai ni mahaifina na rika kuma...
  Hmmm ysnzu dai ki nuna min kowa ki fada min matsayin su gurina kinji
 Tana share hawaye tana jan majina tace to zan nuna maka kowa
   Wannsn baffa idi,baffa ibrahim,da kuma abbi sune yayyan ummin mu
To ashe kice baffan mu dai ba ke kadai ba kin sha kulawa me yawa lokacina ne yanxu fa .
  Hah lallai ma hamma mubarak
 Au me sunan malsm kar dada ta bige min bakina na kira sunan mijin ta.

Aka sa dariya gaba daya to kuma na dawo gareka
 Hamma yusuf,hamma nas,hamma masdook,,hamma ni'imatullahi duk yayyan ka ne su
Se wannan hamma kamal ta fada tana dungure masa kai shekara daya ya bsni kanin ka ne sakona ne
  To kice ni din dan dangi ne ina da yanuwa da yawa ah sossai ma
  Wayanan yan matan duk sakokna ne fa kannen ka ne su din fadimatu zahra'u,mariya,ni , rabi'atuda kuma amira dukkan mu kannen ka ne.

Wai kice nima bsbba ne uhm man
 To hamma ina matan ku?
Tukuna dai hajiya amma yanzu tunda mun zo gida se ayi yar gida ko kuwa ya faruk?
Faruk murmushi yayi kawai dan shi din miskiline komai sede yayi murmushi baya wani uhm bare uhm uhm kawai aishsn yake kallo yana godewa Allsh daya bashi kanwa
  Shi kennan ma baffa in ka tashi aurar dasu hamma nas seka hada da hamma faruk da mubarak au me sunan malam ko dada

Ni de ki bsrni kawai nayi ta kallon ku kuna shakiyanci kuna raha yadda zan kuma yarda cewa *zumincinmu* ya d'ore in kara kallon ku in kuma godewa Allah da ya d'ayyaba min zuri'ata ta kara ha'baka.
Amin dada

Masdook ya mike ya yi bakin kofa yace ke xo mana! Yayi waje ta mike tace ina zuwa hamma to se kin dawo.

Ya zauna cikin yan'uwan sa yana hira shi ksm ya zage se zuba yake ana bashi labari kala kala shi kam se kallon fadimatu yake yi a fakaice a ransa yace niksm nayi mata a kumo da izinin Allah
Yayi murmushi kawai ita ma tana lura dashi wani irin kallo yake mata ta kasa nutsuwa.

Yusuf yace amira kije ki huta haka naga kwana biyu ba kya bacci da wuri saboda waccan akun me shegen surutun tsiya
   Dariya tayi kai hamma hira muke kawai a tsakanin mu ta yan'uwa kasan in muka koma se kuma wata haduwar!
  Ni de kije ki kwanta dada ki mata magsna ina lura da ita bata hutawa ga uban sanyi da take sha kwana biyu bata jin magana ta
   Ke amira uwata tashi kijeki ki kwsnta ki dinga jin maganar mijinki kin ji ko
  To dada
Dada wai mijin ta ne?
Eh man mu ina xamu bar yara su fi haka girma bs a dakin mijin su ba
 Gaskiya ne kennsn dukksn su sunyi aure ?
Da gayya yayi tambayar dan yaji.ko fadima ma nada aure
  Eh su biyun ba da aishan da amiran
  Harda aishata?
Eh
Kennan hamma masdook ne mijin nata?
Eh shi ne fa ashe mun girma dai
Eh ksm
Ke fadima ku gysra dakin yusuf su huta haka sun sha hanya

 to dada,bara na gysra musu dakin.
Ya bita da kallo faruk ya masa wani murmushi dsn ya fara dago dan'uwan nasa.
Shi kumma ya sunne kan sa.

****
Hannun ta ya kamo yana murzawa ya jata har bakin motar sa ta a ciki shi ma ya zagaya ya kunna motar ya jasu
 Ta juyo tana kallon sa hamma ina zamu haka?
 Siyar dake xan yi
Ta kulle bakin ta tayi masa gum 
Mutum da matar sa a tambayesa ina ze kaita
 Kayi hakuri
Shiru ya biyo baya .

Farka motar yayi ya fita ya zagaya ya fito da ita muje mu ko
  Hamma
Ni ban san gsrdama muje mu
Binsa ta dinga yi ya bude wani gida suka shiga ts juyo tana kallon sa a ranta tace ikon Allah

Daki ya shigar dakin ya sa ma dakin key yana kallon ta ita ma shi take kallon dan karin bayani take nema daga gurin sa
Biris ya mata ya shiga toilet dan yayi wanka zaunawa tayi zugum tana kallon kasa
  Wayarta ta dauko ta kira amira taji ta a kashe bata da carji

Tsaki tayi yafi a kirga ya fito daga shi se towel ta juya masa baya ya bude drower ya dauko short da singlet ya zura ya fesa turare ya shafa mai me tsada ya kalleta ki je kiyi wanka
 Ni ba wani wanka da zan yi gida xani
To nan a daji kike ?
To ni dai ksna ganin danuwana yaxo memakon muyi hira seka wani dauko ni nan
  Kefa aisha naga alama baki da tausayi baki da imsni ko
  Ni mena ma
Ba kya tausayina dubi yadda kike kiba ni kuma dubi yadda nake ramewa shekaru nawa ina kallon ki kawai kamar hoto bazaki ji tausayina ba ki bani abunda nake so ki maidani namiji ko!

Hamma ai ban da wannan karfin
Mtsw kin san Allah bazan barki ba yau ki gama tsaretsaren ki da kumbiya kumbuyiyar ki amma kin gama zuwa hannu

Yau sena amshi sadakina kums na nuna miki *sakomakon kauna*

 Aisha humaira dai kawai kallon sa take yi kawai cike da mamaki
Da tsoron masdook din.

Ke banda abunki abunda kike gudu ai a ksn sa auren ya ta'allaka dashi ya dogara
  Hawaye suka zubo mata a kuncin ta
 Ki daina kuka muyi addu'a Allah ya barmu tsahon shekarun da zamu ga jikokkin mu
  Kice amin.
Ta masa banza
Kinga ki je kiyi wsnka ki zo muyi sallah

_bayan wasu mintuna_

Wankan tayi tasa wata riga da ya bata ta fesa turare sallah suka yi ya ksma kanta ya mata addu'oi sannan ya mata tambayoyi
 Daukarta yayi cak ya dora kan gado ya dinga raba ta da kayan jikin ta ita kam idan ta a kulle yake taki kallon sa se hawaye da take zubowa

  Rungumeta yayi ya dinga aika mata da sakonni kala kala masu rikitarwa da rudarwa da rikita wanda ake yiwa numfashi kawai yake fitarwa ita kuma kuka kawai take dan ba karamin gurzuwa take yi ba a gun sa gaba daya ya gama kashe mata jiki tun dare ake sbu daya be barta ba seda yaji kiran assalatu shima dan sallah ba dan ya gaji ba

Da ya dawo ma gun ya sameta ya ita ko tunani take yi girman daren farko duk yadda zata fassara daren farko bazai fassaru ba wata irin kauna da soyayya da ba a taba sanin bil adama yana yiwa dan uwan sa bil adama ba,ita ce yau hamma ya nuna mata.
Tun farkon daren har zuwa karshen sa .

Ji tayi ya rungumeta a kirjin sa cike da wata kauna ,ta sa hannu tana goge hawayen ta ya na taimaka mata yana mata fatan alkhairi .

_ina son ki aisha humaira kin yadda ke din zuciyata ce ,my heart kin yadda?_

*a sanyayye ta amsa ,na yarda*
Murmusawa yayi ya dada rungumeta
  Ta hankada shi
Dubi fa iriyar wahalar da ka ba ni ,kalli fa ciwon da ka mini.ni don Allah ka bari na warke .
  Janyota ya dada yi gaskiya kam naga alama kin sha wuyar ,kiyi hakuri kin ji ko !
Ni nasan kina sona ni ne da wawa mara hankali dana tsaya wasa da damata se Allah ya rahamace ni ya fargar dani da mata ta gari ki yi hakuri duk wannan whalar na dan lokaci ne .
Ita dai kuka kawai take yi yace aa heart kukan ki bana so ni kadai nasan me nske ji in kina saukar da hawayen ki
To naji kai ni nayi wanka
 Mu koma gida kafin a fara neman mu
 Ta kuma fashewa da kuka ni ka cuce ni kowa yanzu ze san me muka yi ka bani kunya ba seka bari se mun koma kano ba
  Ke baki da kirki wallahi in bari har se mun koma kano ai kafin lokacin ya rayuwata  zata kasance?
Da wa zan kuma lulawa wannan duniyar maji dadin.?
Ta hararesa ,

_cike da shagwaba ta ce to ai ni bani da lafiya baka ga yadda nake ji ba_

To yi hakuri  "oh!sorry,
Na gani ayi hakuri a yafewa masdook mijin aisha
 Ranar se lallaba ta ya dinga yi ta shirya se azahar yace su zo su koma gida ta dinga surfa masa harara kamar idan ta ze sauko kasa
  Yo in kin harari masdook ai kanki kika harara dan kin zama ni na zama ke kima bari kar a mana dariya a ce mun samu sabani saboda na amshi hakkina na shekaru daidai har shekaru bakwai da yan wattani ina fama da ke
    Ya shafi mararta Allah sa a kokarin farko na samu na farke wasan dukan hannun sa tayi
  _Ayi hakuri hajiyta my heart!_
[6:27PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*Aisha humaira*
✨✨✨✨✨✨✨
*Na*
*Khairat up*
*67*

   Hajiya
Na'am ahmadu
Hajiya jibi faruk da mubarak zasu dawo fa ah alhamdulilahi naji dadi kace na fara shiri
Jikokina zasu dawo
Wallahi kuwa hajiya ina tunanin zan je gun aunty maryama na sanar mata seta zo ta taya ki wasu yan ayyukan ko kuwa
  Ni ba wadda zata zo ta tari dana guda daya rak fa ehe ni da raina ba za a raba ni da dana tilo ba
  Wai mardiya yaushe zaki yi hankali
Hajiya ina ganin girman ki kar ki shigo maganar da ba naki ba kin ji ko!

Mardiya wa ya baki izinin zuwan min gida?
   Ta ja dankwalin ta gaba ta dan karkace yin kaina ne saboda naji dana zai dawo shi ne nazo na ji takamaimai ran da zai dawo
  Ai baki da d'a a gidana!
Tayi shewa,weee ai ko kasuwa ta tashi dan koli dai ya ci riba
 Mardiya in kin gama haukan ki kina iya bar min gida na ban yarda dake ba sabida haka yi waje kiyi ta shirmen ki na sani ko bayan fita ta ki lahanta min uwa
  Lallai ahmad ban ga laifin ka ba
Ko ki fita kona sa a fitar min dake daga gidana
Dadin abun nima ina da gidan uba
Nagode da kika tuna da haksn seki fita wannan gidan ahmad ne
  Tana kumbure kumbure ta yi waje ya yi sallama da hajiyarsa sannan ya fita.

Hajiya ta zauna zugum tana tunani can hawaye suka zubo mata Allah jikan *aisha humaira* yarinyar kwarai me kirki me girmama mutane Allah ksi haske kabarin ki ban da rabon kuma ganin ki amma ina sa ran insha Allah zan ga takwarar ki alfarmar annabi da qurani.
    ******
Ya faruk!
Na'am mubarak ya akai?
Ya faruk wato ina son muyi shawara dakai muhimiya
Ina jin ka ,
Ya faruk ina ganin in mun sauka a kano zan wuce katsina
Katsina?
Eh katsina
Me zaka yi a katsina?
Zan je gun yar'uwata ne
  Amma dea ya muka yi da kai da abba ina cewa mun wuce gurin an bar maganar
 Anyi haka amma zuciyata ta daure da yawa yanxu kuma ta.kai makura baxan iya jurewa ba ina son ganin yar'uwata kar na mutu ban ganta ba ko sau daya
  Kana tunanin zasu amshe ka ? Zasu gane ka,ko ita xata maida ka wa?
 Ya faruk duk ban san wannsn ba amma ina ji a jikina yar'uwata bazata kini ba kuma karfa ka manta jinin mu daya
  Ya faruk nasan duk abunda ya faru kaddara ce wadda bawa baya wuce ta abba ma na son ganin diyar sa haka nima
  Nima ina da bukatar ganin ta yadda take yar'uwar ka haka take nawa ba sai ka fada min cewa ciki daya kuka fito ba ko ka tuna min *a sanadin* mahaifiyata hakan ta faru
  Aa yaya wallahi ban kawo haka ba kayi hakuri
 To tare zamu je da kai saboda haka yau zamu yi booking gobe mu tafi yadda zamu yi kokarin komawa da wuri kar abba ya farga yace mun raina shi.

To amma ya xamu fara lalunben gidan?
Shi ne ai
Da sauri yace inna(maryama)
To ya zaka yi tambayar ta fada maka
  Uhm shi ne matsalar
Why not mu tambayi baba sunusi
 Owk
  Wayar kawunun nasu ya kira bugu biyu ya dauka
 Hello baba
Hello,faruk ya shirye shirye?
Lfy baba
To madallh baba dan Allah tambaya zamu yi
   To Allah sa na sani
Baba dama ina nemsn kwatancen gidan su mama na ne
Amma mesa kk tmby?
Kawai amma in bazai samu ba...
Aa zan turo ma ta text
Tom baba ngd.

Meya ce?
Ze min text din adress din
To alhamdulilahi
Amma Allah sa kar ya fadawa abba wannan maganar amin dai .

**
Amira wai meya ke damun ki naga se amai kike kwana biyu lafiya dai ko
Eh nima dai ban san dalili ba kullim yanzu kasala bacci da amai da zazzabi duk ke damuna
Kin fadawa hamma?
Aa
To ki fada masa a duba jikin naki
Tom bara ya shigo
Aa ba wani bara na kira shi a waya nasan yana kusa ko hamma masdook
Ki barsu fa
Saboda me?
Saboda nasan meke damuna
Ah ah me ke damunki ?
Ciki ne dani fa
Wane irinc.....se kuma ta daka tsalle omg na shiga aljjana ciki oh dear na kusan zaman aunty
  Bakin ta ta kulle mata ki daina ihu kar a ji
Aa to ai abun murna me bana tsiya ba
Na sani ina kunya ne
Tab baki ji kunyar daukar cikin ba se kunyar a sani
Ke fa dadi na dake kennan shakiyanci
   To bazan fada ba amma zan gayawa my honey bee ya san maganin da za a baki
Kin fiya kafiya wallahi mstw
To naji
*****
Kamar yadda suka fada haka aka yi direct motar katsina suka samu shata su biyu kawai zuwa dikko har inda suke nema .

Tafiyar hour biyu ds rabi suka yi dake me motan gudun tsiya yake yi.

Basu sha wuyar gano gidan ba dan an san su sannannu ne ba boyyayu ba a unguwan.

Su baffa na gona su kuma mazan suna waje dam basu koma gun aikin su ba

Faruk da mubarak suka karasa da sallama
Wa'alaikum sallam
Dan Allah nan gidan mal.mubarak dikko ne?
Eh nan ne kunzo daidai dui jikokin sa ne a nan
To alhamdulilahi mu baki ne
Ai naga alama inji nas
Yanzu gunwa kuka zo dan shi mal din ya rasu tuni sede matar sa *(dada)*
Eh gunta muka zo
To bara na mata iso.

Shi ko yusuf kallon sa kawai yake yi se mubarak yace ina ni'imatullahi?
Gashi nan shi ne ni'ima
  Kawai murmushi yayi nas kuma ya shiga gidsn dan fadawa dada tana da bako

Salamu ailkum
Wa'alaikum sallama
Kai nasiru ya akayi tsohuwa gunki nazo kinyi samari a waje sun zo zance
Jefan sa tayi da dakuwa dan banza su wsye samarin kasan cewa ni din ma fa yar gayu ce
Ah sossea ma kin samo gredin samari
Cene su shigo mana kun barsu a waje dan shashanci
 Au daga abun arziki

Ku shigo
To ya raka su har bangaren da dada take tana lazimi ne dama

Yana shiga kawai tsayawa yayi ki kam.yana kallon ta
itan ma shi take kallo
Takalminsa ya cire ya shiga ciki kawai dada ya rungume yana kuka
[6:27PM, 3/14/2017] Kairat Up: [21:30, 01/03/2017] Khairat: ✨✨✨✨✨✨✨
*Aisha Humaira*
✨✨✨✨✨✨✨
*na*
*khairat up*
*70*
*_daga fadar_*
     *Hikima writers _*
*_association_*

_wannan page din na ko wanne masoyin aisha humaira ne_

A haka suka koma gida dakinta ta shiga ta samu ta kwanta daga baya kuma zazzabi ya kamata me zafi sossea ita kanta dada bata yi tunanin ta dawo ba tana gun wata kawarta me kalwa a makota

Da kan shi ya shigo bangaren dada ya leka ba kowa ya kara gaba zuwa cikin dakin ta a kwance ya sameta a rufe da bargo jikinta se rawa yake yi.

Jikin ta ya taba yaji zafi rau tsabar zafi taba jikin yayi subahanallahi my _heart_ ya haka naji kina zazzabi
  Bata ce masa komai ba se kuma hawaye suka zubo mata ta juya masa fuskarta a ranta tace *kai ka jawo*

  Bara ina zuwa dakin sa ya koma ya dauko firat aid ya xo ya auna zazzabin yaga ya kai 120 ya zare idan sa ya kuma aunata da kyau

Bara na samo miki magani kinji
 Uhm kawai tace masa yana fita ya hadu da mardiya matar hamma isma'il
  Ina zuwa baban mama?
Wallahi humaira ce bata da lafiya zan je chemist na siyo mata magani zazzabi take
 Wayyo ina dada?
Dada bata nan
Bara naje to.kamin ka dawo
Da kin kyauta min.

Dakin ta shiga ta sameta sannu aisha sannu kin ji?
Uhm
 Meya sameki ne haka
Adda ba komai *(kina ganin ina zazzabi zaki wani tambayeni meya faru)*ta fada a ranta.

Be jima ba ya dawo ya mika mata madarar youghrt bata ta sha se ki bata maganin nsn ta sha
To me baban mama
Ya fice ina zuwa.

Maganin ta kalla ta kalli humaira wai kina nufin se yau?
   Hararta tayi a fakaice
Ungo ki sha bara na samo miki dettol da ruwan zafi ki shiga
 Ni baxan wani shiga dettol ba yana da effect
  To sena sa miki gishiri zaki ji dadin jikin ki
Komai ta hada mata ta shiga ruwan kina yi kinji se gurin ya warke
To adda
Bara naje na turo miki su amira dan basu san kin dawo ba
To
Ki dan ce ma hamma ya kawo min kifi kiyi mini farfesun kifi kinji?
To bara na duba ko yana nan.

Basu jima ba suka shigo dakin amira tana ganin ta tunsurewa tayi da dariya lallai yau bakin wata ya mutu amma hamma ya burgeni yau ya amsa hakkin sa
  Cikin rawar murya da kyar tace zan baki amsa duk sanda na samu sauki adda kuma gulma mtsw ni ku fita ma kawai
  Tohm.

***
Da daddare suna hira a dakin tsakar gida dake waje maxan su da matan su tare da kamal yana bawa mubarak labari shi ko faruk yana danna computer din sa 
  Mubark ya ga yadda aisha ke harar masdook shi kuma yana folding din hannun sa alamar tayi hakuri murmushi yayi kawai duk da yana son magana da ita su biyu kawai
  Ya gyara murya hakika naji dadin ganin dangina masu hadin kai da sanin ya kamata tabbas nayi.rashi amma ina sa ran da izinin Allah duk abunda na rasa zan same shi a iya dan lokacin nan
 Amma gobe zamu.koma kumo
 Aisha ta kyabe fuska hamma zaku koma kuma bamu fara hira da kai ba bamu ma xauna ba fa
  Eh kamawa tayi kanwata shi yasa kin san abba besan mun dawo ba kuma besan mun zo garin nsn ba
  Daga ina kuke to?
Daga cairo muke
Karatu?
 Aa aiki muka yi ma abba a can dama gobe ya kamata mu dawo amma saboda ina son ganin kanwata na karya dokar abba na zo nan nida ya faruk
 Kennan abba bsya so ka gani shi ma ya gani?
  Idanta ya ciciko da hawaye tayi kalar tausayi
 Shi kuma ysyi kasa da kansa
 Ficewa tayi daga dakin tana kuka
Masdook ya mike ze bita
Mubarak yace hamma can i?
Komawa yayi ya zauna a kasan carpet din.

Shi kuma ya bita
Rabi'atu ta kalli faruk gaba daya burgeta yake yi miskilancin sa ya tafi da ita gaba daya
 Fadima ta zungureta me haka?
Ba komai
A kunne tace fada min ko de mr.miskili ya miki ne?
Hararta tayi suka sa dariya
[09:09, 02/03/2017] Khairat: *71*

Shi kuma yana gefen ta yana jin su se ya gyada kan sa yana murmushi dan yaji su sarai ya cigaba da aikin sa.

Humaira a dakalin dake bakin bangaren su baffa ibrahim ta hade kai da gwiwa tana kuka se shassheka ta ke yi
  Ya xauna ya mika mata hanky din sa ta amsa tana shsn majina ta dinga gogewa
  To kanwata kukan me kike yi kuma?
Bsyan ga wan ki a kusa dake ?
  Uhm ni ba wani kusa dani bayan tafiya zaka yi ka bar ni kai baka sona abba ma bsya sona ina zan kama ni kam?
Kiyi hakuri humaira ba haka bsne
To yaya  ne?
Hamma babana baya son ku ganni ta kuma fashewa da kuka ta rungume shi tsna kuka
  Shi ma hawayen yake yi
Amma yayi sauri ya goge hawayen sa humaira abba ba kin ki yake ba kullum cikin kewarki yake
To amma me dalilin sa na kin zuwa inda nake.kusan shekaru nawa?
 Hmm !circumstances ne ya jawo ba laifin kowa ba ne  kaddarar mu ce da jarrabawar Allah ki daina cursing din kan ki ko.kina ganin laifin abba a wannan lokacin ko waye aka fadawa wannan maganar zai yarda uwa fa humaira uwa!
 Hmm banga laifin ki ba humaira amma ki daure a cikin wani kwana na zuciyar ki ki yafe ma abba bazan ce ki yafe ma umma ba amma zan iya neman wa abba na alfarmar nan  inji faruk
  Gefenta ya zauna ta zamo tana tsakiyar su ya share mata hawayen ta kinga duk bamu san dadin kanwa ba se yanzu kuma kina ta kuka baki bari mun sha hira ba haka kike so mu tafi ko laifin su abba ne ya shafe mu ko kuma ni ne baza ki kula ni ba saboda umma na
  Uhm'uhn ni kukan zaku tafi nake
To ba kya so mu tafi mu dawo miki da abba da hajiya kaka?
 Da gaske?
Ya gyada kan sa hmm
Ta yi ihun dadi amma zan yi kewar ku
 Muma haka ko zski bimu can?
Wooo ya faruk ai hamma bazai bari ba ai kuma dada tace se abban yazo tukuna zanje kumo  se Allah ya kawo ku
    Toh kice akwai kewa a gaba
Gaskiya kam
Amma hamma mesa baku zo da matan ku ba?
Dariya suka sa gaba dayan su faruk yaja hancin ta ke muke jira ki nemo mana matan
 Haba !
Sossai ma amma ya fada yana sosa keya kamar mubark ya samu mata a dikko fa
  Ta ware ido haba dea yaushe yazo yaushe ya fita dazai samu yar dikko,
    A gidan dada mana fad....
Mubarak yayi maxa ya kulle masa baki haba ya faruk ka bari mana
Hannun sa ta janye daga na ya faruk fada min hamma bar me sunan tsohon nan
  Da gaske nake gaya miki fa ya gano rama daidai dambun sa a gidan takwaransa
 Ta jijiga kai lallai kam *zumunci dangin kauna*
 Ai kar ka damu bari komai ya saisaita zan fadawa dada
Ke kam kin biyewa ya faruk ko wasa yake
Au baka son fadimatu?
Yayi shiru yaki tankawa dariya suka sa masa suka dinga hira a tsakanin su
 Hamma masdook dake jikin bango yana kallon su ya dinga murmushi lallai ba abunda ya fi dan'uwa dadi yau dai ga humairar sa tana tare da yan'uwan ta na jiki suna wasa da dariya suna sa ta nishadi ba karamin dadi yaji ba
  Komawa daki yayi ya kwanta dan yana bukatar hutu dan kuwa humaira ta shaysr dashi jindadin duniya Allah miki albarka *_aisha humaira_*
[6:27PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*aisha humaira*
✨✨✨✨✨✨✨
*na*
*khairat up*
*72*
*_Daga fadar_* *©*
*_hikima writers association_*

🌹for someone close to mah hrt🌹
   Komai na rayuwar aysha da masdook ya canja komai daidai kamar ba su ba kullum se tayi waya da faruk da mubarako ta video ko ta waya
   Hakq ma suna gaisawa da hajiya ta waya.
 Kamar yau da wuri ta shirya dan tana da papper ta safe ta shirya ta samu masdook yana jiran ta a dinning bata ma ci abincin ba ta riko hannun sa tana ja ka taho mu tafi am getting late
Ok mrs.kin dau komai na shiga exams din ne?
 *eh na dau komai*
To muje matata
Suna tafe suna hira wayarsa na gun humaira game take yi wata sabuwar num ta shigo ta mika masa yace dauka mana ina driving
  How can i ?
To barta tayi ta ringing amma ba dadi hamma to ya kike so nayi shld i stop driving?
 To bara na dauka .
Hello,
Hello ina me wayar?
Aka tambaya daga daya bangaren
Kirjin humaira ya buga ta kalli masdook
Ya?
Kai ake nema
Na sani aisha ai wayata ce in bani ba wa za a nema ?
Uhm
Waye a layin?
Nima ban sani ba in mun sauka ka yi redailing num ka ji waccece!
Ta ajiye masa wayar nsn da nan mood dinta yayi off kamar ba humairan sa ba.
 Se yayi shiru yasan sauran
 Yana sauketa bata tsaya wata wata ba ta fita ta doko masa kofar
Yace wow!
Yau ina cikin wani hali.

Da kyar ta rubuta exams din ta na jin bakin ciki takaici duk ya isheta ranta har wani suya yake yi mata muryar wannan yarinyar kawai take ji na mata yawo
  Da kanta ta koma gida ranar ta yi wanka ta ci indomie da kwai ta kwanta kan 3 seater ta lumshe idanun ta
 Tana jin saukar motar sa amma ta sha mur ta ki bude idan ta
     Ya harde hannayen sa a kirjin sa
To wai ke ba abun dadi bane mijin ki yayi kasuwa?
 Hararsa tayi to ni ina ruwana?
To mesa kike damuwa?
Ba ruwanka da damuwata
 _Ya zaki ce bnda damuwa da damuwarki bayan damuwarki tawa ce tawa kuma taki ce_
 Tsaki ta buga ta mike stop flattring me?
To ni a su wa?
Zata yi dakin ta ya ce sorry matas kiyi hakuri khadijatul iman ce ta kira ni
 Khadija kuma?
Yep khadija ce ta kirana wai tana kano kuma zata zo anjima
 IT taxo yi a asibitin nasarawa
  Kuma kin san dangantakar mu da ita bazan iya ce mata aa ba sabida matsayin umman su gun mama
 *(yar kanwar mama ce)*
  Kuma ta rasa inda zata zauna se a nsn ina fa sane da irin kallon da take maka in tazo dikko nidai kawai.raina min hankali zaku yi sabida ga banza ko?
  Oh God humaira ki...dakin ta ta shige ta kullo masa kofar a fuska
  _zaunawa yayi a kasa kawai ya dau robar ruwa ya kwankwada ya dau wayarsa ya kira khadija din yana tambayarta tana ina ki ta kusa karasowa?ce masa tayi ta bata ya tambayeta tana ina ta masa kwantace ki jira zan turo nas zan miki sending num sa kuyi contacting juna ya kawo ki na riga da na dawo gida kuma kin min nisa to hamma ina jira kar ki damu yana ajiye wayar kira num nas ya masa bayanin inda take basa num ta ita ma ya tura mata num_
Kuka ta fashe da shi ita kanta tasan yadda take jin kishin masdook a ranta musamman ma khadijan nan ta rabu da zainab ta samo iman.
  Mtsw mutum se kyan tsiya mutum ayi ta rububin sa amira ta kira a waya ta mata warning
To ni ina ruwana
Da ruwan ki kawai ki kirata a waya ki mata warning a kan ta nesanta kanta daga wajan mijina
To aunty ayi hakuri ni mijina ya dawo zan masa girki.

 Wayar ta watsar a kasa ta shiga ta kuma yin wanka tasa riga doguwa pink ta daura gashin ta da blue ribbon ta fesa turaren ta me kamshi ta dauko orbit ta sa a bakin ta falon ta koma ta zauna tana gani har wanka ya sake
  Ta hararesa au harda canja mata wanka?sabida ta ga iya dashing din ka?
Ko kallon ta be ba ya cigaba da dane dane a wayarsa ta kuma kufula dashi seta shiga kitchen
 Dariya yayi kasa kasa  yana zaune nas ya shigo da khadija suka zauna ya masu sannun da hanya
 Ruwa da lemo da snacks ta kawo musu ta zauna suka gaisa da khadija din kowacce ta ciki na ciki barema humaira da taji kamar ta maketa dan takaici se wani yauki take tana wani iyaye shi kuma dan tsokana ta dinga mata wani salo ai se aisha ta fashe da kuka ta shige dakin ta nas da masdook suka sa dariya suna tafawa
*_women i tell u_*
Khadija da daki a can side din gefen wancan ki shiga ki huta kamin anjma na dasa briefing dinki aikin
To bara na huta tukuna
  Nas wallahi akwai daru  a gidan nan har se na samu aisha ta yarda ba komai tsakani na da khadija
kyaleta in dai humaira ce seta saka hawan jini kai ai kila in an auna yanzu za a ga ya hau ba mamaki ma ya yi high da yawa
 Haba dan Allah sa wasa
 Nan suka dinga hira a tsakanin su.
[6:27PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨
*na*
*khairat up*
*71*
*_daga taskar_*
*_hikima writers* *_association_*

Da asuba suka shirya dan timing din su yayi daidai da lokacin flight dinsu na cairo zuwa gombe din.

*_kumo_*
Shirye shirye sossai suka yi dan zuwan yaran nasu biyu da maryama da hajiya suka yi shirye shiryen kaysn soye soye da kuma abinci kala kala
  Abban nasu yana office yana duba consinment na takalman da za a tura can cairo din ya buga waysr yayan shi sunusi ya fada mishi imformation na flight din da zasi biyo da karfe nawa zasu sauka dan ayyukan sun masa yawa office din nasu *(AISHA HUMAIRA&SON'S SHOE'S FACTORY)*
wannan reshen su dake kumo kennsn akwai ma a katsina,kaduna da zaria yanzu kuma suna yin import export da kasassashen ketere kamar su us,cairo,london da turkey dalilin zuwan su faruk garin kennan.

*katsina*
Kinyi kyau fa hajiyata
Uhm ina kukan ne nayi maka kyau
   To na gaji da cewa kiyi shiru se kuka kike yi mubarak din in ce ya ce miki zasu dawo da abba?
Uhm!
To me kuma na kukan?
Kawai ina kewarsu ne
Kai humaira u re immpossible duka duka hour su nawa da barin garin namu?
   Two
Then?
Ba komai
It better be ba komai din zan fita amma ki kasance cikin shiri daga yau zuwa gobe zamu ko na bar ayyuka kin bar makaranta.

To seka dawo
Allah sa.

*~some hour's later~*
*~4:30~*
Suka karasa garin gombe baba sunusi yana jiran su a airport yana ganin su ya washe bakin sa dan dadi tare suka shiga mota motsr ta daga zuwa gari kumo
 Ya hanya?
Alhamdulilahi baba
To masha Allah ai naji daga bakin abbsn ku anyi singing contract din ko
Eh anyi jibi ma muke sa ran maida musu kayan ma kila ya faruk ne ze kai musu .
To Allah ya yarda
Amin.
Ina ma yau aisha na nan da ranta data ga yadda yaranta suka zama
 Hmm baba
Uhn ina jinka?
Baba sunusi munje katsina
 Munje dikko
Ya juyo baya yana kallon mubarak
And who on earth gave u guys the order?
 Baba ....ina kewar yar'uwata da yan'uwana zuwa wannan lokacin shi yasa naja...
  Munje tare nida shi kuma decision dinmu ne mu biyu dan muga yar'uwar mu
 Amma kunsan in ahmad yaji wannan maganar seya ji ba dadi ya hukunta ku
 Baba a wana littafin aka rubuta cewa kar dan'uwa yaje gun dan'uwan sa saboda wasu dalilai marasa kwari ?
  Hmm faruk kayi min shiru in yar 'uwar ku ce mu iyayanta ne
  Laifin ku daya for hiding it.
 Ba dan wani abu muka ki fada muku ba illa saboda munsan baxaku bari muje ba
  Hmm a bar maganar se munje gida amma ban son ku sanarwa ahmad wannsn maganar?am i clear?
Uhm
Gud
****
Hajiya da maryama sun ji dadin gani su sunje lafiya sun dawo lafiya
 Ta cika su da snacks da abinci
kai hajiya irin wannsn gara ai se mu kasa tashi
 Ai haka nake so
 Hajiya
Uhm ina jinka
Hajiya nida ya fsruk munyi muku laifi
To daga dawowa?
Me kuka aikata?
Munje dikko
Da sauri ta juyo tana sakin cup din hannun ta kallon su ta dinga yi dayan bayan daya dan jin karin bayani .

Maryama tace duk a yaushe kuka je?
 jiya muka je muka dawo yau
*OMG*
kun san me kuka yi kuwa?
In ahmad yaji magansr nsn
Aunty mun gaji da wannan rayuwar ta wahala mun gaji
Inji faruk taya muna da yar'uwa amma mu kasa ganin ta shekara kusan ashirin da daya kennsn amma bamu santa ba ku tausaya mana da kun ga yadda taji dadi da ganin mu ba
  Amma...
Kyale su maryama sun yi daidai sun girma ai
 Inji ahmad ashe ya dawo yana jin su
Bani ruwa na sha dan Allah aunty
To ahmad sannu da shigowa youwa
  Ya zauna wani satin za a tura consignment din suks amsa da to
  Yana shan ruwan ya buda fulas ya debi abincin ysna ci
Ku kuma fa baxaku ci wani abu ba ?
Ko ba kwa jin yunwa?
Junan su suka kala cike da mamaki ba haka suka zata ba
  Mubarak ya dauko wayarsa ya tura text wa abban su
Yana jin alamun shigar sako amma be duba ba seda ya gama cin abincin tukuna
  Ya dauko wayar ya duba hoto ya gani a kasa kuma an rubuta
     _kanwata aisha humaira ahmad kumo_
Murmushi yayi amma silently a fakaice se kuma ya maida wayar sa cikin aljihun sa ya mike hajiya zan shiga na huta
To ahmadu seka fito
To.hajiya.
***
_hajiya ta ce mubarak fada min ya jikata take?_
_hajiya kinga hoton ta ma kyakyawa ce kinsan kamar su daya da abba ya fada ysna nuna mata hoton aisha humaira hawaye suka taron mata a ido na dadi yace kingan ta ko me kyau ga surutu in fada miki kinga wannan hoton kinsan waye tare da ita?aa fada min mijin ta ne haba miji?eh mijin ta kuma yayan ta kace kun sha hira da ita ka fada mata labarina?uhm uhm na fi so kuje ku gsnts ds ksnku ta ganku kums dan tana kewar ku da yawa musammsn ma abba dan Allah ki lsllaba abba kuje inda take wallshi tana son ganin abba_
_ban san ya zanyi da ahmadu ba tsoro yake ko me Allah kadai ya sani nsyi magiysr amma yaki zuwa aunty mariya ta amshi wayar masha Allah tabsrkallah tayi kyau sossai mubarak ya adda? Tana nan lafiya tana gaishe ki_
 _Allah sarki dada ta fada ta share hawayen ta_
_dakin sa da ya shiga wayar sa ya dauko kawai ya duba hoton da kyau ba karamin kama suke da juna ba shi da its kamar photocopy din sa alhamdulilahi Allsh nagode maka daka bsni wannsn kyauta Allah ta jiksn ki aisha Allah kai rahama kabarinki tabbas kenmata ce me hakuri matar kwarai daga ksn ki ban kuma yin wani aure ba bazan iya bawa kowa darajr ki ba nayi rashin mata ni kadai nasan yadda nake ji a raina wajan nisanta kaina daga diyata amma komsi yayi fsrko zai karshe hsr ya zamo labari zan je na samu diyata na nemi yafiyarta na bata duk wata kulawa da bsn bata ba a lokacin da take da bukata_
_Ya share kwallar sa ya shiga wanka_

~FALO~
kai mubarak kira ta mana ka fada mata mun karaso lafiya
au na manta wallahi nasan tana can tana zuba ido a screen din wayar ta
 Shi yasa na ce ka kira ta
Eh kirata nima naji muryar jikata!
 Kiranta ya soma yi yasa a handsfree bugu byu ta dauka lokacin tana kwance kan masdook yana shafa mata kan ta suna hira
Hamma ya bugo hamma ya bugo ki dauka mana to kar ta tsinke au
 Hello hamma ya kuka je gida? Kunje lafiya ko?ya hanya kunci abinci? Kun huta?
Hamma masdook ya dungure mata kai ke sokuwa ce wallahi ki barshi ya amsa daya se tambayoyi kike aika masa wanne ze ji?
Au am so exicted kawai
 Ta murguda masa baki ni ba sokuwa bace
 Mubarak yayi murmushi yace ya fsruk kana jin su ko sun fara ai aisha da surutu take
  Mun xo lafiys lou kuma muna kewar ku ku dukka
Muma haka ga hajiya ku gaisa da ita
Tom
Hajiya ina wuni?
Lafiya lou aishatu ya gida ?
Lafiya lou hajiya kaka nan fa kuma suka fara hira a tsakanin su.
 Har bacci ya fara daukan ta
 Maddook ma sun gaisa da ita hajiyar.

Ba karamin dadi naji ba hamma wajan gaisawa da hajiya saura abba na rungumeta ysyi sannsn yayi peacking din ta a goshi muje na raka ki gun dada kar ki min bacci a nan ki jsza min daukar ki ga nauyi kina da
 Kirjin sa ta doka yayi tarin karya kai ai kece action humaira din don karfi suna hira suka shiga cikin gidan har dki ya rakata ya koma nasu bangaren.
Yana shiga yaji sako ya shigo masa
    _mr.arrogant gudnyt and i love u ♡_
  Smiling yayi
 _it's mr.arrogant saying gudnyt to mrs .arrogant love u to ♡_

*_washe gari_*

Dukkan su a dakin dada suna hira suka yi break ana ta hira da misalin karfe shabiyu suka shirya da nas da amira da humaira da masdook da yusuf dan komawa gida zasu sauke su amira sannsn su wuce kano

Amira ta tsaya ta window ta rada wa humaira abu a kunne suka kyalkyale da dariya
  Masdook yace ai se anyi gulma ai se anyi ni na sani
Se anjima kuje lafiya
amin.

Da suka isa kano ma sun sauke nas a gidan shi tukuna sannan suka koma gida suna shiga ya rungumota yana shinshinar jikin ta tana nokewa hamma bara...shhh kar kice komai daukarta yayi cak ya nufi daki da ita ya kwantar da ita ksn gado ya soma romancing dinta ta ko ina dana ga zai lula wata duniyar sena ja musu kofa na kulle na koma masu gadin gidan dan be kulle kof ba saboda zumudi.

Se wajan magrib suka fito suna sheki sunyi kyau tana sanye da karamar top da short haka shima suks xsuns
  Ya zaki zauna kums
To mezan yi
abinci mana
tab wallshi na gaji sede ka girka mana yau ja gajiyar dani kuma amarya nake ba aikin da zan yi ma 😜
   Kin fiya ragwanta humaira ko zs a yi second round ne
Hah! Wallahi kai mugu ne ya juyo yana mata cakulkuli ta dinga dariya dan Allah ka bari hamma dan Allah to waye zeyi girkin?
Ni zanyi amma seka taimaka min Allah jikina ciwo yake kai din janab bana wasa bane
  Haka nake so ki san cewa mijinki gwarzo ne a ksn ki
 Uhm aiko na sani

  *_weekend mubarak_*
       _daga khairi_
[6:27PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*Aisha Humaira*
✨✨✨✨✨✨✨
*Na*
*Khairat up*
*73* *©*
*_daga fadar hikima writers association_*

_don't listen to the saying of eyes,those eyes also decives,try to identfy the right eyes that suits u_
   
    Seda ta gama kuksn ta sannsn ta fita falo ta zsuna yau bata da niyan dora musu girki ma sam sam aisha me kike nufi ne?
A ina?
Girki dare nayi
And ?
Kallon ta kawai yayi ya gyda kansa ya shige daki jim kadan ya fito tare da khadija ya dau key din sa ya yi waje aisha se mun dawo tsabsr takaici da bakin ciki kasa magana ma tayi ni hamma ze wa wannan wulakancin?
  Shi kuma resturant suka je da khadija suka ci abinci tare daga nan ya kaita gidan kanin baban ta dake dawaki road suka gaisa da matan sa sannsn suka yi yahuza suya ya siyo nama da youghrt ya dawo cikin motar saura na ice cream ya fada yana murza hannayen sa ya biya ta oisis ya siyo ice cream din sannan suka tafi gida.
  Be samu humaira a falo ba amma yasan tana daki ya shiga dakin bayan sunyi sallama da khadija kan ta shirya da wuri gobe wajan takwas zasu wuce asibitin baya son african time na mata
 To hamma seda safe Allah tashe mu lafiya amsa ya bata ledar ta sannan ya leqa dakin bata nsn kennan tana dKin sama
 Saman steps ya hau ya shiga dakin ta tana kwance ko a ksn kujera tana tunsni kan sa ya girgiza ya karasa kusa da ita ya tsuguna a kasan kamshin turaren sa shi ya isar mata da sakon shigowarsa dada kulle idan tayi
  Haba sweet mata ta ni na isa kallon wata da sunan soyayya bayan ke kin san fa matsayin khadija a guna ko dan darajar mama bszan hanata zama a gida na ba nasan aishata will understand me fahimta ce ke aisha humaira ki cire zargin cewa akwai wata bayan ke a cikin rayuwata  insha Allah da yardar me duka me kowa da komai kin gama samun masdook kina ganin a iya wuni daya gaba daya na rame na zama abun tausayi saboda rashin samun kulawar ki humaira ta a taimaka a min afuwa kinji matata kanwata anminiyata
   Ni ka rabu dani ai ban ce ma komai ba kinji yadda zuciyata take bugawa dari dari kawai aisha take kira ke ni in banda shirmen ki ta tuyo tana kallon sa aa ai magana zan miki ba ba a nake miki ba ta murguds masa dan bakin ta in bsnda abunki humaira me zan kalla a sauran mata gaki komai ya ji baki san matsayin ki ba da girmsn ki a gareni ke ni duk sauran matan nan muna mata nake ganin su.
   Ai dadin baki ko hamma kai expert ne a yin sa
 Kinga naman nan na sanyi daure muci ki sha ice cream din su mu cigaba daga inda aka dora ba abunda kiks ci fa yau ina kallon ki
  Ai baka damu na ci din ba ne
 Wai kin san ko yadda nake ji dake har fushi naso nsyi irin wadda na saba yi ta da in koma masdook muhammad dikko na da amma a ksn ki na kasa kin gama da rayuwata  wallahi humaira ban san irin son da nake miki ba humaira.

 Bani naman ta amsa tana ci tana gamawa ta mike ta yi hanyar wadrope ta dauko towel da gown ya yi maza ya bita ya hadata da wardrope din ya soma aika mata da kissises ta ko ina na jikin ta huma...ir..a kiyi hakuri ki tausaya min ya sa hsnnun sa ya zare mata zip din rigarta tsugunawa tayi a kasa ta runtse idanta gam gam heartbeat dinta yana bugawa gudu gudu sauri sauri.
   Seda yasan yadda yayi ya lallaba matarsa suka lula duniyar maji dadi.
***
_bayan wata daya_

Dada na zaune a tsakar gida ita da inono da mardiya matar isyaku suna tankade dan yin girkin dare
  Sallama suka ji daga waje
 Ta amsa tare da cewa a shigo
 Yana shigowa dada ta mike cike da mamkin wanda take gani shi kuma tsugunswa yayi har kasa ya gaida dada bata idda amsawa ba ya sa gwiwowin sa a kasa ya hade hannayen sa biyu ya na zubda hawaye ya ce
   *dada na jigata haka,na wahala,na gaji,na kasa kara dannewa,na kasa bin abunda nayi alkawari na daina kunyar na daina zagin kaina a daki kawai abu daya nake da buksta yanzu kafin na koma gun mahilicina hakki yana damuna dada ki tausya ki yafe ni da aikin dana aikata dada kin kasance uwa me tarin kulawa ga yayanta da basu tarbiya kin kasance uwa me tausayi da hakuri dada ki yafe ma wannan dan naki a sanda abubuwa suka faru dada shaidan ya shiga tsakani ga kaidin mata dada abu daya idanuwana suke da muradin gani abu daya kunnuwana suke da bukatar ji abu daya hannuwana suke da bukatsr tabawa dada ki yafeni in ga humaira dada ki yafe ni inji kalmar abba daga bskin humaira dada ki yafe ni hannuwa na su rike na humaira dada jinina nake son gani dada ina da komai amma bani da komai na rasa aishata ruhina bazan koma gun Allah ba ban ga jinina ba jinin aisha*
  Mike tsaye ahmad bari kuka haka aisha ai taka ce ni ban hanaka aisha ba illa na rike alkawarin marigayiya ne ahmd duk abunda ya faru mukadiri ne daga Allah kuma ta faru ba yadda za ayi dama ni laifin ka da nake gani rashin waiwayar mu da kayi ka watsar da al'amuran diysrka kasan da ita kuma ahmad ni bana kin ka domin kai din abunda aisha ke so ne ban san mesa kaki zuwa inda take ba ko sau daya amma a nan kuskuren ka yake na watsi da diyarka wadda ko hula baka taba aiko mata ba baka san yarintar ta ba baka kuma san girman ta ba baka san halin da take ciki ba da dai baka sani ba shi ne an zalince ka amma kasan da ita Allah ya kiyaye gaba
  Dada baki zuwa ba da gayya illa ina bin alfarmar da aisha ta nema a gurina
 Aisha ta tura min da wasika ta hannun aunty
 Eh tabbas ni na bada wannan takarda.
  A cikin takardar aisha ta nemi alfarma a gurina
 _bana kin ka ahmad kuma ban dau abunda ka min a matsayin cin fuska ba illa kadarata kuma ko kadan ban rike ka ba ko dan darajar hajiya bazan ki jinin ta ba ahmad ina gadon asibiti nake rubuta ma wannan wasikar tamkar wasiya ce na baka ahmad na soka kuma bszan daina ba naso munyi wata rayuwa me tsawo me dadi da fadi da kwanciyar hankali sede Allah be nufa ba bazaka manta dani ba ko dan yara biyu da na bar maka ka rike_ _mubarak ka kula dashi amma diyar dana haifa bazata iya xama a gidan ku ba sabda matar ka bazan yarda a hallakata ba_ _dan ba abunda bazata iya ba amma ina neman alfarma a_ _gareka ka min wannan hallacin in har ka taba sona koda inci daya ne ahmad ka_ nesanta kan ka daga _gun diyar dana haifa har se ta kai munzalin_ _da ya kamata kasanta wato bayan girmanta ka nesanta ta daga_ _wahala da bakin ciki na gidan ka ka bar min ita gun dada ban son_ _wata alaka ta hada ka da ita har se sanda ta mallaki hankalin ta_ _duk tsiya zata neme ka ina so ka bawa mubarak labarin_ _rayuwata a gidan ka ina so ka rike shi_ _amana ka hada kan sa da danuwan sa faruk don duk yayan ka ne karsu raba kan su ka rike su amana in zaka iya ka koya wa kan ka rashina da rashin diyarka ina son ka ahmad kayi kokarin gyara gidan ka na barka lafiya taka har abada aisha humaira mubarak dikko_

 Dada taya zanki bin zancen aisha to na kai kasa bazan iya ba ki bani diyata dada
  Ahmad kar ka damu aisha ai dama taka ce sede tana gidan mijinta a kano
  Hawayen dadi suka zubo masa ya riko hsnnayen dada dame zan saka miki da wacca kalma zan gode miki dada kin gama min komai dan kin rike min amanar diyata dada Allah saka miki da alkairi ya sa ki gidan aljanna ba abunda zan iya saka miki dashi dan girman ki ya wuce misali.
   Ahmad shiga ka zauna a ciki bara a sama maka abu kaci ka sha hanya ina hajiyar taka?
 Tana kumo amma jibi zasu zo da su mubarak
To masha Allah
Allah ya kawo su lafiya amin .
 Nan aka fara hidima da shi a gidan su baffa ma nan suka same shi suka dasa wata hirar ta ya bsyan rabuwa.
  A nan dada taji ma ai sun rabu da tsohuwar matar tasa tun tutuni da daddewa ma.
 *****
*KANO TA DABO*

Hamma
uhm
Ina ji a jikina wani abun alkairi na bina
Uhmyayi murmushi haka ne humaira
Kasan me?
Uhm uhm sekin fada
Hamma mubarak yace min yana da surprise da ze min
To me wannsn
Nima ban sani ba wallahi amma am excited naji me ze min
Nima kinga kin sani a suspense
ai gwara se mu shiga suspence din tare ni da kai mu dukka
 Ya yi kissing bakinta ai kece mu dukka din
ta ja hancin sa
Ouch kin fiya cin zalli fa
Ta masa fruny face yayi dariya mara ji kawai
  Ya shafa dan cikin ta yaushe zan yi ajiya ne naga kullum aiki ne amma har yau ba result lafiya ko.
Kai zan tambya kila aikin naka beyi sossai
 Kai lallai ma ke din nan duk akin danake kina korata kice baya yuwuwa?zaki sani yau in na kamaki ki sekin ce dan Allah  in bari ku huta
   Ta sa masa dariya
A nan suka yi ta hira tana tsokanar sa yana basarwa daga karshe ya sunkuceta ya yi daki da ita.
   Asuba ta gari masoya.
[6:28PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*Aisha Humaira*
✨✨✨✨✨✨✨
*Na*
*Khairat up*
*74-75*
*daga fadar*
*©* *hikima writers association*

Da misalin karfe uku da rabi na rana aisha zaune ita kadai ta dawo da wuri dan lecture daya kawai suka yi ta gama sakwara se nishi take dan daka dan ma maigidan yace shi yake so yau da bazata yi ba bata son dakan sakwara tayi miyar agushi taji nama da kaza zako zako a ciki da busasshen kifi yaji kayan hadi da gyada a ciki ta jera tebur kawai jiran dawowarsa take tadan kishingida taji tsayuwar motoci kusan guda biyu ta ce aa yau da bako yazo min?
  Ta cigaba da zama seda aka buga kararawa tukuna ta mike cike da zumudi ta duba ta dan ramin kofar taga hamma mubarak da hamma ni'imatullahi a tsayi da sauri ta bude tayi wani ihun dadi
 Sannu da zuwa hamma sannu da zuwa
 Kafin yace oh ke kam kin fiya ihu ba cewa mu shigo ciki?
To mu shiga hamma ya hanya?
Suna shiga wata motar ta kuma tsayawa
 Yau ksm kace gidan nawa ya yi albarka su waye kuma?
Da dada,da mijinki,da hajiya,da aunty maryama,da baffa idi da baffa...bari bari fada hamma nasan housefull kuka zo min ki tsaya mana kiji da wa kuma
 Aa i cant gwara na karasa na gan su da ido na dada fa kace ka barni naje na yi tsalle kanta
 Yana dariya ta fita daga falon tayi waje da gudu wani tsalle ta daka kan dada tana ihu sannun ki dada kingan ki yau a gidan aisha humaira naji dadin ganin ki
  Humaira ki na nutsuwa mana
 Hararsa tayi cikin wasa
 Ya maida mata
Baffa idi ya mata dakuwa
Tayi kasa da kai taja dada zuwa cikim gidan bakin ta yaki ruhuwa dan murnar dadin ganin dada

Aisha kina da bako fa a waje baki kula ba?
   Bako kuma,waye?
Wani bawan Allah ne
To bara naje na ga
    Aa zauna masdook shigo dashi
Ai tunda suka shigo tare da hamma masdook ta saki baki galala tana kallon sa cike da mamaki da al'ajabi ta kalli wannan ta kalli wancan
  Ma..
Dada Abbana ne?
Uhm shi ne aisha abban kine ahmad ne yazo ganin diyarsa
  Hawayen da suka taron mata a fuska suka karasa zubowa se kuma ta mike ta karasa kusa da shi tana hawaye
  Ashe zan ga abbana?
Ashe zan gan shi a duniya na furta wannan kalmar ta abba?
 Ya Allah !Allah nagode maka Allah nagode maka kaine abun godiya kai ne me yadda kaso a san da kaso a lokacin da ka so dada,hamma,yau ga Abban *aisha humaira*ina kallon sa yana kallona wanda zan kalla nace Abbana
   Ta rike hannyensa ta dora goshin ta a kam su tana hawaye
 Abba ka dade baka zo ba
Ka nisanta ni da kiran ka da suna abba
Abba ni me nawa a sabanin ka da ummina da dada ?
Da har ta shafe ni ban samu arzikin cin yarinta da ku ba bayan ina da dangin uba
 Abba *ba a min adalci ba* a *rayuwa ta* da ka hane ni da sanin *waye kai a gareni*
Abba soyayyar uba nada muhimmanci a rayuwar ko wanne dan 'adam bayan ta uwa abba ni mesa baka yi tunanin ko da daga nesa ne ka kalle ni ko ka min magana ko ka gan  ni?
Abba bakin jinina ya kai haka?
  Yana hawaye ya girgiza mata kan sa kiyi hakuri humaira ni na kasance me laifi a gareki ban san mezan ce miki ba ban san da wane ido zan kalle ki ba ban san ta ins zan fara neman ahuwar ki ba aisha ki yafe ma mahaifinki da ya yi rashin kula da d'iya kamar ki
   Abba ka daina fadin haka ni nasan komai ka gani daga Allah ne yanzu lokaci ne abu daban lokaci ne na farin ciki abba nagodewa Allah da ya kuma hadani nida kai nasan waye mahaifina
  Yau duk wanda zai min tambya cewa ni din *yar waye*zan ce ni din diyarka ce abba zauna kaji
   Ta cika masa gaba da kaysn ciye ciye
 Yana fara'a yace duk ni kadai humaira?
Uhn abba na
 Hajiya tace ba a ta kaka ko?
Ai ku kun tsufa
Aka sa dariya
abban naki se ya rigani cikawq ni ina nan tare dake
Humaira tayi dariya lallai ma hajiya sannu
Masdook yace hajiya gaya mata kin fita kwari ita sabuwar jini ku tsohon hannu
 Aka yi dariya gaba daya dakin.

Nan hira ta kacame ta bayan rabuwa ana ta raha kamar kar a rabu
    _dama komai yayi farko zai karshe har ya zamo labari komai na zaman duniya dan hakuri da juna ne da zaman lafiya_

Da daddare ko suna hira suna cin tuwon shinkafa da miyar kubewa danya cikin tray daya
 Aisha ta kalli hamma mubarak tana dariya hamma
uhm aisha
Kulle
Kamar ya?
Kai de kulle?
Uhm cas
Tom
Youwa abbana
Uhm aishata
Abba kayi wa hamma aure shi da hamma faruk
Kema kya fada sun fara tsufa ba magaji na gaji da neman masu mata ke kila kya samo musu
 Sossai ma abba ai sun yi mata fa sun rufe ka ne basu sanar da kai ba
 Aisha me haka?
Me kuwa gaskiya zan fada musu ne ayi da wuri ko kuwa nasan fa kuna so kuna kaiwa kasuwa
 Eh lallai ma yarinyar nan
 Abba da fadimatu ta gidan mu da rabi'atu
 Kee aisha sharri inji dada
Wallahi Allah dada da gaske nake miki in kuma sun karyata dada ki tamaye su kiji
  Megidana wai haka ne
 Shiru yayi be tanka ba dan aisha ta gama dashi wallahi shi kuma kunya ce dashi kamar me
   Ka fada min faruku haka ne?
Dada ni mezan ce?ai tunda ta fada hakan ne
 Kinji ko dada kawai se munzo neman aure dikko
  Masdook ya mintsine ta a baya ta zabura wayyo Allah na hamma mena ma?
Ai da sauri yayi waje dan aisha zata kunyata shi cikin su baffa aka sa dariya
Dada tace meya miki?
Mintsini na fa yayi?
  Kowa ya s driya wayanan yaran halin su sai su yan banxa
 To ai shi kenan mu dama haka muke su a dinga *zumunci* Allah ya tabbatar da mafi alkhairi
Amin dada
 Ahmadu mu kuma daginmu sun kare a dikko ta katsina
 Aiko dai hajiya gashi nan dai zuri'ar tamu daga kumo zuwa dikko Allah dai ya kara tabbatar da mafi alkhairi a zamantakewar mu ina jin dadin wannsn *yanayin*Allah dai ya sada mu dukka a gidan aljanna
amin ya Allah
[6:28PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*Aisha Humaira*
✨✨✨✨✨✨✨
*Na*
*Khairat up*
*74-75*
*daga fadar*
*©* *hikima writers association*

Da misalin karfe uku da rabi na rana aisha zaune ita kadai ta dawo da wuri dan lecture daya kawai suka yi ta gama sakwara se nishi take dan daka dan ma maigidan yace shi yake so yau da bazata yi ba bata son dakan sakwara tayi miyar agushi taji nama da kaza zako zako a ciki da busasshen kifi yaji kayan hadi da gyada a ciki ta jera tebur kawai jiran dawowarsa take tadan kishingida taji tsayuwar motoci kusan guda biyu ta ce aa yau da bako yazo min?
  Ta cigaba da zama seda aka buga kararawa tukuna ta mike cike da zumudi ta duba ta dan ramin kofar taga hamma mubarak da hamma ni'imatullahi a tsayi da sauri ta bude tayi wani ihun dadi
 Sannu da zuwa hamma sannu da zuwa
 Kafin yace oh ke kam kin fiya ihu ba cewa mu shigo ciki?
To mu shiga hamma ya hanya?
Suna shiga wata motar ta kuma tsayawa
 Yau ksm kace gidan nawa ya yi albarka su waye kuma?
Da dada,da mijinki,da hajiya,da aunty maryama,da baffa idi da baffa...bari bari fada hamma nasan housefull kuka zo min ki tsaya mana kiji da wa kuma
 Aa i cant gwara na karasa na gan su da ido na dada fa kace ka barni naje na yi tsalle kanta
 Yana dariya ta fita daga falon tayi waje da gudu wani tsalle ta daka kan dada tana ihu sannun ki dada kingan ki yau a gidan aisha humaira naji dadin ganin ki
  Humaira ki na nutsuwa mana
 Hararsa tayi cikin wasa
 Ya maida mata
Baffa idi ya mata dakuwa
Tayi kasa da kai taja dada zuwa cikim gidan bakin ta yaki ruhuwa dan murnar dadin ganin dada

Aisha kina da bako fa a waje baki kula ba?
   Bako kuma,waye?
Wani bawan Allah ne
To bara naje na ga
    Aa zauna masdook shigo dashi
Ai tunda suka shigo tare da hamma masdook ta saki baki galala tana kallon sa cike da mamaki da al'ajabi ta kalli wannan ta kalli wancan
  Ma..
Dada Abbana ne?
Uhm shi ne aisha abban kine ahmad ne yazo ganin diyarsa
  Hawayen da suka taron mata a fuska suka karasa zubowa se kuma ta mike ta karasa kusa da shi tana hawaye
  Ashe zan ga abbana?
Ashe zan gan shi a duniya na furta wannan kalmar ta abba?
 Ya Allah !Allah nagode maka Allah nagode maka kaine abun godiya kai ne me yadda kaso a san da kaso a lokacin da ka so dada,hamma,yau ga Abban *aisha humaira*ina kallon sa yana kallona wanda zan kalla nace Abbana
   Ta rike hannyensa ta dora goshin ta a kam su tana hawaye
 Abba ka dade baka zo ba
Ka nisanta ni da kiran ka da suna abba
Abba ni me nawa a sabanin ka da ummina da dada ?
Da har ta shafe ni ban samu arzikin cin yarinta da ku ba bayan ina da dangin uba
 Abba *ba a min adalci ba* a *rayuwa ta* da ka hane ni da sanin *waye kai a gareni*
Abba soyayyar uba nada muhimmanci a rayuwar ko wanne dan 'adam bayan ta uwa abba ni mesa baka yi tunanin ko da daga nesa ne ka kalle ni ko ka min magana ko ka gan  ni?
Abba bakin jinina ya kai haka?
  Yana hawaye ya girgiza mata kan sa kiyi hakuri humaira ni na kasance me laifi a gareki ban san mezan ce miki ba ban san da wane ido zan kalle ki ba ban san ta ins zan fara neman ahuwar ki ba aisha ki yafe ma mahaifinki da ya yi rashin kula da d'iya kamar ki
   Abba ka daina fadin haka ni nasan komai ka gani daga Allah ne yanzu lokaci ne abu daban lokaci ne na farin ciki abba nagodewa Allah da ya kuma hadani nida kai nasan waye mahaifina
  Yau duk wanda zai min tambya cewa ni din *yar waye*zan ce ni din diyarka ce abba zauna kaji
   Ta cika masa gaba da kaysn ciye ciye
 Yana fara'a yace duk ni kadai humaira?
Uhn abba na
 Hajiya tace ba a ta kaka ko?
Ai ku kun tsufa
Aka sa dariya
abban naki se ya rigani cikawq ni ina nan tare dake
Humaira tayi dariya lallai ma hajiya sannu
Masdook yace hajiya gaya mata kin fita kwari ita sabuwar jini ku tsohon hannu
 Aka yi dariya gaba daya dakin.

Nan hira ta kacame ta bayan rabuwa ana ta raha kamar kar a rabu
    _dama komai yayi farko zai karshe har ya zamo labari komai na zaman duniya dan hakuri da juna ne da zaman lafiya_

Da daddare ko suna hira suna cin tuwon shinkafa da miyar kubewa danya cikin tray daya
 Aisha ta kalli hamma mubarak tana dariya hamma
uhm aisha
Kulle
Kamar ya?
Kai de kulle?
Uhm cas
Tom
Youwa abbana
Uhm aishata
Abba kayi wa hamma aure shi da hamma faruk
Kema kya fada sun fara tsufa ba magaji na gaji da neman masu mata ke kila kya samo musu
 Sossai ma abba ai sun yi mata fa sun rufe ka ne basu sanar da kai ba
 Aisha me haka?
Me kuwa gaskiya zan fada musu ne ayi da wuri ko kuwa nasan fa kuna so kuna kaiwa kasuwa
 Eh lallai ma yarinyar nan
 Abba da fadimatu ta gidan mu da rabi'atu
 Kee aisha sharri inji dada
Wallahi Allah dada da gaske nake miki in kuma sun karyata dada ki tamaye su kiji
  Megidana wai haka ne
 Shiru yayi be tanka ba dan aisha ta gama dashi wallahi shi kuma kunya ce dashi kamar me
   Ka fada min faruku haka ne?
Dada ni mezan ce?ai tunda ta fada hakan ne
 Kinji ko dada kawai se munzo neman aure dikko
  Masdook ya mintsine ta a baya ta zabura wayyo Allah na hamma mena ma?
Ai da sauri yayi waje dan aisha zata kunyata shi cikin su baffa aka sa dariya
Dada tace meya miki?
Mintsini na fa yayi?
  Kowa ya s driya wayanan yaran halin su sai su yan banxa
 To ai shi kenan mu dama haka muke su a dinga *zumunci* Allah ya tabbatar da mafi alkhairi
Amin dada
 Ahmadu mu kuma daginmu sun kare a dikko ta katsina
 Aiko dai hajiya gashi nan dai zuri'ar tamu daga kumo zuwa dikko Allah dai ya kara tabbatar da mafi alkhairi a zamantakewar mu ina jin dadin wannsn *yanayin*Allah dai ya sada mu dukka a gidan aljanna
amin ya Allah
[6:28PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨
*Na*
*Khairat up*
*76-78*
_*©*_
_*daga fadar*_
_*hikima writer's association*_

   Kwanan su uku a gidan su masdook suka tarkata da kewar juna suka koma garuruwan su yan gombe suka dau hanya yan dikko ma suka dau hanya
ba karamin dadi humaira taji ba dan zuwan abban ta da yayunta maza guda biyu ita ma yanzu alfahari take da dangin ta
  Har an samu anyi maganar auran hamma mubarak da hamma faruk abbsn da baba sunusi zasu je dikko neman aure.
  Allah sa ayi damu.

***
Cike da kasala ta take kwana biyu tankar ba ita ba ga uban bacci da zazzabi ta take yi da ciwon kai.

Har kusan karfe tara bata farka ba wanda ba sabon ta bane masdook har ya shirya ya ja mata dan yatsa
  Ta dan juya alamun baccin be isheta ba
  Humaira lectures din fa?kin ga kin makara nima baki min break ba baki tayani na shirya ba kwana 2 naga wani sabon alamari kika fara mun a gidan nan kin fara wasa da komai ko?
   Hmm!hamma na gaji wallahi baccin be isheni ba ka hada tea ka sha kaji?
  Kallon ta yayi ya sunkuyo kusa da fuskarta meke faruwa matas?
   Hankade shi tayi ni ka daina zuwa kusa dabi ban san wannsn turaren ko ta fada da tsawa tsawa
 Mamaki ya ciks shi ya kufula kawai ya dungure mata kai ya dau jakar sa ya kara gaba
 Ita kuma ko a jikin ta komawarta baccin tayi abunta .

Yarinyar nan bata da kunya wallahi mtsw.
 
***
   Humaira bata farka ba se wajajjen karfe daya da rabi na rana tayi salati ta shiga bandaki tayi wanka ta zura atanpa doguwa ta koma falon nan cikin ta ya fara kugin yinwa yana zillo tsaki tayi dan wani irin 'kiwa take ji
  Wayarta ta lalubo ta danna number din hamma masdook yana duba mara lafiya lokacin se be dauka ba har ta tsinke
  Tayi tsaki mtsw
Shi kuma da ya gams da mara lafiya ys tafi yin sallah saida ya dawo ya kuma ganin kiran ta kusan missed call goma
 Ita kuma wannan lafiya?
Kiran ta yayi da sauri ta dauka tana dauka ta fashe da kukan shagwaba ni shi kennsn tun dazu ina kiran ka bska dauka ko ?
 Shi ne abun kuka
Uhn uhm ni yunwa nake ji .
 Hah'ah ,kina jin yunwa humaira ki shiga kitchen mana!
  Ni baxan iya ba
Ya kike so ayi yanzu?
Ni alala nake so na gwangwani ka kawo min
 Humaira ban son fitina fa da tashin hankali wane irin alele ina zan samo miki ki daure ki tashi ki gyara ki dora ki ci ni kuma ki min tuwon shinkafa zan dawo da wuri ban san wani alele
Ai seta sa mishi ihun kuka wallahi ba abunda zan yi ka siyo min kawai ta kashe wayar.

Kan sa ya dafa ni in banda rigima da masifa humaira ina zan samo miki wani alala tsaki yayi ya dau mukulinsa ya shiga office din wani abokin aikin sa dr.muhammad isa zage
 Yana gurnanin masifa kawai
Ya dai mijin aisha humaira?
Hmm wai alele take so ni ban san me yske damunta ba kwana 2 se rigima take ji abu kadan fada da masifa in ta gs dama kuka ga tashi a latti.
 Ya dinga murmushi
Ya ina ma bayani kana min murmushi?
To ai kaine ma masdook banda abunka ai kai seka godewa Allah ka raba goron murna
  A wannan tashin hankalin da nake ciki zan raba goro?anya kana jina kuwa zage?
  Wai idan ka ne ya rufe ko kan ka ne ya kulle?
Kamar ya
Duk ka fado alamumin masu ciki kuma ksna neman answer da ka riga ka santa.
  Alamomin masu ciki kuma...... la'ilaha illa lahu ai zama be kamani takalmin sa ya zare ya kalli gabas yasa goshin sa a kasa yana nuna godiyar sa ga Allah bakin sa har kunne zage amma naji dadi tashi mujr nemsn abuncin gargajiya dan Allah
  Tsaya in kira mrs.dita ince ta aika a siyo yadda in mun karasa an karbo ko kuwa kar aje ya kare
To maxa yi sauri kirawota.

***
Wajan karfe hudu da rabi ya dawo yadda ya sameta ya basa dariya sossai
 Tana zsune jigum a kasa ta ware kafafuwa tana shan iska dankwalin a kasa bakin ta a tsuke tana kuka shame shame
Duk yunwa ta gama mata kamu ta na ganin sa ta mike zumvur ta karasa kusa dashi ta fara duksn kirjin sa da karfin gaske ta dinga mintsinin sa
 Yau naji mugunta aisha wannan ai cin zali ne kashe ni zaki yi?
  Ba kaine ka min fada a waya ba bazaka samo min alele ba ina ta kaina nima ina zan iya maka wani tuwo
 To yi hakuri zauna ys zaunar da ita ya ajie mata flask din alele a gabanta
 Tana budewa kamshin ya daki hancin ta ba karamin dadi taji ba gashi yaji manja kusan guda goma taci ya tsaya yana kallon ta wai aishar sa na dauke da babyn sa a ciki kwansa kwallar dadi ta zubo masa a fuska
 Ysna kallon yadda taje ta lodar abinci aishar da ba ta wani ci sossai
  Aisha ai se kiyi kiba irin wannan cin abinci haka kamar an aiko ki?
  Uhm bazaka gane ba hamma yunwa nake ji sossai na rasa dalilin wannan cin nawa yayyi yswa
  Bara nayi wanka na duba lafiyar ki
 To hamma kar kasa wNnan turaren kaji?
To ur highnesss na daina sawa
Ta washe masa baki nagode.

Wanka yayi yasa 3quter da singlet ya fito da kaysn awo ya auna  ta ya ya duba plus dinta da komai da ya kamata ya koma daki ya ajiye
  Ya dawo falo ya sunkuce ta sama ya dinga juyawa da ita a duniyar sama janati(lol)
Humaira mu godewa Allah sarkin sammai da kasai mu godewa Allah da ya bamu ikon na ganin wannan ranar da kunne na yaji wannan dadadan albishir din kema zan jiyar dake
  Hamma ajiyeni kaina ta juya ajiye ni
 Ys zsunar da ita kan kujera ya riko hannayen ta biyu ya sa kunnen sa a cikin ta yana hawaye saukar ruwa taji a jikinta
 Hamma kuka?
Kukan dadi ne humaira kukan dadi ne barni na gama dan kin gama min komai kinsan ko babbsn rana gun ko wanne da namiji a duniya da abunda zai fi son ji a duniya?
Uhm me kuwa sama da matar sa tana son sa kuma ya sameta kuma gata da ladabi. Duk ba wannan ba humaira ba moment me dadi irin moment din da nake ciki yanzu moment din dana fuskanci na kusan zama *baba*ba momont me dadi irin moment din da zan ji wannan kalmar daga bakin abinda zaki haifa msna *BABA* wallahi humaira kin gama min komai
  Wai ni ban gane ba me kake cewa ne?
 Abunda nake cewa shi ne aisha humaira ta kusan zama *UMMA* kin kara takawa matsayi me girma daga *'ya*kika xama *kanwa* daga ksnwa kika zama *mata*daga wata zaki zamo  kuma *UWA*Kinga kuwa kin kara daraja fiye data
  Hamma are u serious?
Kai ya gyada mata
 Ta rungumesa dan dadi ta dinga mika godiyar ta ga Allah hamma Allah ya nuna mana fitowar abun cikina _i want to also experience the moment_
 Murmusa mata yayi to se ki ji sharuda na
    Ban da aikin wahala
    Cin abinci kan lokaci
     Bwn da tsalle tsallen kin nan.
   In kina son abu ki fada min.
Ban da yawo
  _An gama boss_
Saboda ina son babyn nan that will be my first born
 So ki kula sossai ban san abunda zai taba min shi
To hamma i ll be extra careful.
  Youwa banda wasa da ruwa a toilet saboda tsantsi zsn dinga rakaki
To babban baby
 Ke kuwa *_dan so_*
   Hhh
Kinga huta a nan zanje in dawo
 Tom ka taho min da chocolates to da grapes to ds gwanda
 Naji madam kar fa ki mtsa daga nsn.
   To
Rungume filon kusa da ita tayi tsna murnr dadi daga bisani ta shiga tayo alwala ta yi sallah raka'a biyu dan nuna godiyar ta ga Allah.
  Daf da magariba ya dawo ya dinga shigo da kaya niki niki yana ajiyewa a falo
 Ita dai kallon sa kawai take yana ajiye kaya.
 Seda ya gama ya xsuna wash na gaji da yswa
 Sannu da zuwa
Yauwa sannun mu.
  Kinga sakon ki .
Nagode
Wayanan meye?kayan baby ne na wasa kingan su ya juye mata kayan wasan irin na yara su jirage yartsana mota mashun da sauran tarkace dai haka gasu nan
 Su hamma gandoki ke ina rywanki yadda nake jin babyn nan banki ba ya fito ba yau
  Dariya ta sa masa wayanan fa?
Frame ne masu kyau na jarirai ki dinga kalla zaki samu cute babies sannsn wannan radion karatun qurani ne me grma kullum kina ji dan babyn kasance me ilimi kullum kina cin dabino ki sha zam-
 zam
hamma an dau course to Allah amfana amin
se ki rage kallon tv da yawa ban san babyna na kallo over da shan zaki lyk u ya lakuci hancin ta
  Ta dinga dariya nan suka baza kaya suna aikin hadawa
   Daga bisani ya dauko biro da takarda zo mu zabi sunayen yara
 Kai hamma wallahi bada ni ba duk gasu abbi dasu baffa dan rashin kirki kai zaka zabi sunan baby din ka bari ma yazo duniyar msn shi ma yayi kwari cikin
 Ke bar tsofaffin nan zasu sa masa sunaye irin nasu irin su yusha'u su .... ta toshe masa bakin sa kaje ka huta ka gaji da yawa ko kuma fara yanka min gwandar nsn in ci ai ni kuma yanzu na zama bawanki se yadda kika yi dani bara na dauko wuka da plate se kina ci kana bsni a baki dai to madam.

***
Haka rayuwar su take tafiya yadda yake kula da ita har aikinsa yake shiga dan ta fiya kwadayi shi yasa wani zubin yana gida dan zata iya bukatar wani abun kuma kar aje baya nan
  Basu samu saukij laulayin ta ba seda cikin ya yi wata hudu tukuna ta samu sauki amma tayi kiba ta hau kamar ba ita ba tayi jajir da ita
***
   An sa bikin su mubarak wata biyu masu zuwa
  Tana ta lallaba shi ya yarda taje dikko da kumo yaki ya ta bari in ta haihu seya ksits ganin daki
  Kai.hamma fadimatu fa da rabi'atu
Ko ma amira ce
 Ai lokacin nayi wata shidda ai yayi kwari by then baya son gardama yace Allah ya kaimu amin.
[6:28PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨
*na*
*khairat up*
*78-79*
 *_©_*
  *_daga fadar hikima writer's association_*

  _yan uwa kuyi hakuri nayi kuskure wajan rubuta number 78 a maimakon 77 shi yasa na gyara a nan da fatan mun tashi lafiya?_

Cikin aisha humaira na da wata biyar aka fara shirye shiryen bikin su fadimatu amma masdook ya hana taje tun ana sati bikin seda ta fadawa abbi da mama tukuna ya kaita amma duk motsin ta yana jin ta yana ganin ta baya barin ta yin komai.

Lokacin cikin amira watan shi takwas saura wata daya ta haihu ita ma tayi nauyu cikin nata babba kuma se nan da ita hamma yusuf yake yi.

Ranar kamu suka sa wata atampha sharooton sukyi gown a tsakanin su aka kama amaren guda biyu

Washe gari wuni da safe aka daura auren ansha shagali da du dj su aisha ana  ganin rawa ba damar aje a taka dan gam gam ya rike hannun ta yana ta zsre mata ido hamma sau daya
In kin haihu kya yi
Ta zumbura masa bakin sa yayi murmushi.

Washe garin daurin aure wato ran litinin aka dau hanyar gombe yayin da jikoki dada suka sha kuka da fada da nasiha wajen iya zama da miji da dangin miji.

Aisha humaira da amira da hamma yusuf da shi masdook da nas tare suka tafi a mota daya saura kuma a mota daban daban.

Can wajan magrib suka karasa gidan guda daya ne babba kato amma two part wato su biyu ne masu gidan da mubarak da fsruk amma a wajan gidan aka rubuta
   *Aisha Humaira mansion*
 Ba karamin kyau ginin yayi ba da beni kuma kowacce a bsngaren ta dakuna uku uku da toilet ko wanne a ciki kitchen din guda biyu ne daya a sama daya a kasa ba katamin kokarin hada musu kayan kitchen abbi da baffa suka yi ba falon fadima purpule komai kitchen dinta lemon green tun daga fenti har kayan da aka zuba mata a ciki.

Ita kuma rabi'atu pink ne light cikin kitchen dinta kuma purple dark da komai na cikin sa gaba daya.

Ba karamin sha'awa ya bawa mutane ba
   Tun da suka zo aisha ta samu guri ta zauna ta mimike kafafun ta tana ta haki ita ksm ta gaji hamma masdook suna waje su kuma hade da angwayen suna hira

Abinci sun ci har seda suka ture da ksn su da hannun su .
  Kwana abba yace su kuma yi gobe se su koma aka aminta da hakan.

Da daddare suna hira shi da humaira a bsngaren sa ta tsakanin d'a da mahaifi amma aishata ke se kin kwana biyu ko?
  Aa abba gobe zamu koma
 Amma da na so ki kuma kwana ko sati ne se kiyi in yaso kya bi jirgi ki koma gida

Abba sede ka fadawa hamma dan shi ke da matsala bazai barni ba in na tambaye shi kai kuma ko be so ba ze yarda dan kunyan ka
  Aa baxsn masa haka ba in kin sauka lafiya daga baya kwazo mana ganin gida yawon arba'in.
  Shi kennan abba.
 Waysrta ke ringing abba kaga ma ysna kira ai shi baya so nayi nisa dashi ne bara naje ts mike abbsn ya taya ta tashi daga zaune
 Hello hamma
Wai kina ina ne?
Ina gun abba amma gani na fito 
  Kin san dare yayi ya kamata a ce kina bacci ki huta babyn ma ya huta da wuri zamu wuce gobe
 Ai gani nan zan shiga gun su hajiya ko
 Zo tukuna zan miki seda safe
 Hamma Allah da nisa tafiyar fa kasan da kyar fa...
  Lokacina ne baki da shi amma kina dana kowa gud nagode
 Ya kashe wayar
 Ta bi wayar da kallo tana zumburar baki mutum ya gaji ace baze ce ya gaji ba.

****
Da safe aka soya dankali da kwai aka yi kunu aka kuma soys kosai masu shan tea suna sha masu son kunu kuma suka hada da kosai.

Seda suka gama aka yi wanka dan sha daya zuwa sha biyu zasu fara komawa garin su

Abba ya rarraba musu dubu biyu biyu gaba dayan su.

Tun da ta tashi bata ga hamma masdook ba ko a gun break dan tasan haushin ta yake ji to ita ya zata yi ?

Zaman ta tayi kawai.
  Shi kuma se kallon wayar sa yake yi ko zata kira sa amma shiru
 Lallai humaira raini .
Amma ba komai zan rama.

Banza yayi da al'amarin ta shi ma har suka zo tafiya ya wani daure mata fuska ba alamun dariya a ciki se jikin ta yayi sanyi ita kam ta kasa katabus nas ya taya ta shiga baya ta kukuta ta shiga yau sun ga miskilanci tun da suka dau hanyar kano uffan masdookbe fada ba balle yayi tari haka suka yi tafiyar lami sede hira a tsakanin hamma nas da kuma ita humaira din.

Kuma yana jin su har gida ya sauke nas sannan ya maida ta gida ya bata key din yayi reverse ya koma da bsya ya fice daga gidan ita dai bata ce komai ba to mezata ce?tasan laifin ta ne ita ta siya da kudin ta ba wani ne ya siya mata ba.
  Amma idan ta ysyi rau rau da hawaye tana kokarin basarwa amma seda ya zubo mutum se bakin hali da nukufurci

Ciki ta shigs ta zauna ta huta sannan tayi wanka ta dawo ta dafa musu abincin da zasu sa a bakin su tayi lemon kwakwa da kankana ta sa a fridge sannan ta zauna tasa kararun qurani me girma kamin bacci ya dauke ta a ksn kujera tana jin karatun.

Shi kuma gidan abokin sa ya je suka sha hira a tsakanin su kamar ba za a rabu ba se da ya gama ya koma gida yaga tana bacci a gun yasan tayi kewar sa amma yana son yaga iya son da take masa ya koma koya mata hankali kar ta kuma masa haka shi sa ze horata.

Ya debi abincin ya ci sannan ya sha lemo ya shiga yayi wanka ya yi sallah ya kwanta.

Tashi tayi ita ms tayi sallah seta ga alamun an shigo kuma anci abinci wato ya dawo kennsn sallah tayi ta koma dakin sa taga yaba baccin gajiya seta koma dakin ta kawai ta kwanta kan kushin din dakin tana nazari shi yafiya daukar abu da zafi ta shafi cikin ta *babyna u miss dada ryt?*nima i miss him ya daina mana irin wannsn fushin gaskiya amma koda yake laifin moma ne ai shi yasa dada is angry amma zamu shawo kan sa insha Allah.
[6:28PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨
  *na*
*khairat up*
*79-80*

   _tallah_
 
  _a sanadinki yau har asibiti nazo gwaji_
  _wannan wane irin iskanci ne zaki zauna a falo a haka?_
  _ka manta ni yar iskar ce in ya taya ai sena bada kai bori ya hau ko_
     _yana nan tafe_

Kwalliya taci sossai ta sha ado tayi kyau ta zauna zamam jiran sa.sanda ya dawo ya sameta a falo tana kallo yaji dadin ganin ta a haka daga jiya zuwa yau yayi kewarta da babyn shi ya dauke kai ita kuma tayi murmushi ta mike tsaye seta dan gurda kafarta wayyo Allah na wayyo.Allah kafata wayyo...ai da sauri ya karasa gun ta habibaty na lafiya?
Ta zumburo baki da dan shagwaba tace masa uhm ba lafiya ba ba kaine ba kake fushi dani ka ki min magana kayi banza dani da baby?
  To.ai ke kika jawo muga kafan naki?
Ta dora masa a kan cinya kin yi nauyi da yawa
 Ai babyn ne me girma
Ke ba wani dama can katuwa ce ke ni babyna ba ruwan sa
  To tin yana ciki.za a min son kai
Eh to ya zaki yi
Lallai to ban yadda ba se a cire babyn dan baza a raba kasona da babyn ba
 Kin ma isa?wallahi kar ki soma
 Kin san nayi kewar ki da yawa ya za ayi ne yau?
 Ya kuwa ta fada
Ya mata rada a kunne ta ce ohh sede babyn ya vaka
 Kin ji ki ko zo muje tawan my icecream my chocolate my sweer love
 Uhm dadin baki yana jan ta tana komawa da baya ya dauke ta cak a karshe ta dinga dariya tana tsungulin sa wallahi kin zama muguwa wasa wasa.
Ta cije shi a kunne kara yayi yana mata wani kallo.
*****

Bayan wata daya da sati uku
 Amira ta sauka lafiya ta samu baby boy inda aka sa masa muhammad kabeer (kabeer)
 An yi suna an ci an sha an yi rabo yaro yayi goshi.

A katsina aka yi sunsn a gidan ta dan yusuf yace ba bidi'a shi kam a zo masa gida ba za a hada dada da aiki ba ko a nesanta shi da babyn shi ba dan yana da son yara.

****
Komai normal yake tafiya a rayuwar familyn dada kowa sai son barka a cikin wannan shekarar aka yi bikin nas da ni'imatullahi da kamal ko wannen su ya samo mata kuma da gidajrn su ga ayyuka dama suna yi matar sa amina suna kano ne suma tana da fara'a da son mutane shi yasa suka saba da yan gidan su nas haka ma matar ni'ima salma ita kuma matar kamal hauwa'u ita ma akwai sakin fuska.
    Ai dole a saba da dangin dada dan basu da daga kai.

*kumo*
 Fadima da rabi'a ma basa wani kadaici dan mazajen su ksn su a hade yake ga kula da suke basu ga kuma kulawar surukai
  Duk yamma suna babban falo suna hira kamar duk gidan su daya ba hayaniya dake mubarak me barkwanci ne sede faruk da yake dan miskilsnci amma gaban matar sa kamar aku parrot dan magana abun har mamaki yake bawa mubarak fadima tace ina ruwan ka suma suna dauke da juna biyu wata uku uku se jiran ranar da ske jira.

*****
 Watan haihuwar humsira ya kama ba yadda dada bata yi ba ya dawo da ita gida amma yakiya shi baxai iya ba suyi hakuri to hamma ka bsri mana naje gun dada na haihu a can
  Naqi humaira a ina amira ta haihu?
Gidan ta
To kema gidn ki zski sauka ayi komai ansn bazan iya barin ki zuwa wata dikko ba a wannsn yanayin daga baya kya je
 Ai shi kennsn
Uhm naji shi kennsn din yarinya da son yawon tsiya ba kya tunsnin halin kadaicin da zan shiga ciki in kin tafi kin bar ni ke ksn ki kawai kk sani in zauna ina kula dake kawai na wani kai ki dikko ko saboda ga bahon miji
 Oh ni me na ce ina kace ba za a ba?eh to ba shi kennsn ba Allah ya raba lafiya da nsn da can duk daya ne ai.

  Da safiyar yau Allah ya sauke ta lafiya a gida ma haihwar ta zo mata gadan gadan ba karamin kokari tayi ba wajan haihuwa d kanta gashi baya nan a asibiti ya kwana ta rasa yadda zata yi seta kira shi a waya da sauri ya kira abokiyar aikin sa munibah taje ta gyara su da babyn da maman babyn tas suka fito abin su yaron jawur ga hanci kyakkya wa da shi son kowa kuwa.

 Ta sa masa kaya masu nauyi ta sa masa safa ta hannu da ta kafa da hula ta ajiye shi kan gado haka ta taimaka mata ta gyara kan ta suka kwanta gyara bandakin tayi ta fesa masa turar ta wanke da kyau
  Tana fitowa masdook na shigowa yana hamdallah yadda ya ga abar kaunar sa lallai iko na Allah da yawa yake ba a ja dashi muhiba nagode fa aa ba komai ina tukuici na kaga baby kuwa kato jawur dashi
 Haba bani shi na gani ita dai humaira kallon sa kawai take yi tana murmusawq lallai humaira kin iya nukufurci
  Ba matsalq ko muhiba
Eh alhamdulilahi ta sauka lafiya se godiyar Allah amma naji dadi.

Ya masa kiran sallah ya bashi zam zam yasha ya tauna dabino ya sa masa a baki ya yi masa hudubar sunan da zai sa masa
  Hamma meka sa masa?
 *Ahmad*
Ta kalle shi duk sunsn su abbi a tsallake a sa sunan abba?
 Ban son haka ai sunan sa ne
 Uhm kawai tace masa lallai ya mata karamci a rayuwa gashi ma kamr ki daya da shi dan wayo bayan nafi son shi a kan ki
 Dariya kawai tayi tana daga kwance ungo shi bara na kira gida na sanar musu da kyautar da Allah ya bamu
 Uhm gaskiya kam
  Ba a wani jima ba maganar ta karkade dangi autar dada ta sauka lafiya ta santalo ktakyawan saurayi tsoho ahmad aka dinga murna.
Washe gari sega dada da yamma kuma hajiya da maryama suka karaso dasu fadima gida ya cika makil da dangi dan dadi anata barka abban ta ya aiko  da akwati biyu na kyan baby da kaysn me jego an masa takwara.
 Mubarak ma seda yaxo dashi za a yi suna sis din shi ba wani namji an masa aboki aka gysra masa daki ana masa dariya kaji shakiyin uba komai na suna dashi ake da masdook ko kunya.
  In ana ma jaririn wanka masdook ya kafa ido kar a sa masa sabulo ko kunys baya ji.
Aiba kunya a tarairayar d'a aje a sa masa sabulu.kawai a ido ko hanci yayi ta kuka .
  Haka aka yi suna aka watse su hajiya da  dada sune yan zaman wankan.jego ba karamin takura masa suka yi ba sukam gaba daya ya kagu su wuce
[6:28PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨
*AISHA HUMAIRA*
✨✨✨✨✨✨✨
*na*
*khIrat up*
*81*
 *_karshe_*
 *©*
  *_daga fadar hikima writers association_*

       *_the end_*

Kullum da safe da daddare se an mata wankan.jego ita da baby ga tuwon dawa da suke bata wai yana kara karfin jiki ga kunu da take sha.
Yaron ko ya yi kubul bul da shi ga shi ja sak aisha humaira.

Kwansn su dada arba'in da biyu suka fara shirin komawa gida masdook kam tsabar dadi ya kasa boyuwa dada ta masa rankwashi wato murna ma kake ko zamu wuce saboda mun shigar ma hanci da kudundune ko ?
   Kaci kaniyar ka kuwa dan tare zamu tafi
 Ina?
Yawon arba'in
Tab lallai tsofafin nan so kuke ku kashe masdook duk  yadda na yi kewar su
  Ta masa unbola tana dariya sun gama shiryawa daga nsn zasu bini dikko suyi sati su zazzaga dangi bayan sati kuma zata wuce gombe suma ta musu sati sai ta dwo se ka cinye ta
 Kawai kallon ta yake dada har kin tsara?
Sa wasa ko kana da ja ne?
 A'a ni mezan ce miki ai kin gama dani kawai kai ka san wannan kuma ai
  Yaushe zaku tafi?
Gobe da safe insha Allahu nasiru zai zo tare zamu yi dashi dan in anje da kai bazaka bari ayi abunda ake so ba.
 Dada da fin karfi kike wallahi ya fada a ransa.
  Ai shi kennsn Allah kaimu gobsn amin.
  Amma kin shiga lokacina
 Uhm kwa warware in kun dawo
 Yana sosa keya ya shige daki yana dariya
Daga wanka ta fito
  Ahmad na kwance ya sha kaysn masu kyau a jikin sa ysna tsotson hannu
  Tana goge jikin ta tace masa hamma ahmad fa kai ya gada ?
A me ?
Tsotson hannu mana
Kee wallahi zan make ki abunda ya wuce zaki dawo dashi sanda nsyi wayo na ma ina aka haife ki shekara goma sha biyu fa na baki cif cif yar banza
  Ta kama baki tana dariya
   Wai ma waya fada miki ?
Wa kuwa
Hmm dada ko?
Kaima ka sani ai
Ya mike ya dau ahmad din yana masa wasa ta canja kayan ta tana fesa turare
   Kina ji ko gobe zaku wuce
     Dada ta fada min da ksi zamu ko?
Hararta yayi munafuka a zuciyar ki har tsalle take dan dadi ina nan  dada tace ban da ni

  Dada rigima haka zami dau hanya gobe
   Eh

Yaushe zaka zo to zamu yi kewar ka fa
  Tab sede kuyi dan tace se kun dawo ma hade a nsn
  To lallai ma
Kawai ka biyo ni gombe
  Baki da kunya wallahi gidan surukan nawa zan biyo ki
  Zan hakura har ku dawo ya zanyi  nayi kwana da kwanaki ba bare kuma karin sati Allah dai ya kiyaye kawai za a ce
  Amin.
Se tausayin sa ya kamata
Yaron ya fara kuka
Amsa bashi ya shs ya gaji
 To
Yana zaune ysna kallon su yana jin wani dadi a ransa yadda ya ga iyalinsa cikin koshin lafiya seya godewa Allah ya kuma gode masa.
Yana tsotso yayi bacci ta kwantar dashi ta kuma lallaba ta kama mijin ta dan tasan me yake buksta tunda bazata bashi du ba ai ta bashi rabi ma'ana suyi romancing junan su .ba karamin dadi yaji ba ya dinga shi mata albarka yana mata godiya.

Ranar kwana suka yi suna hira a tsakanin su washe gari suka shirya suka gama komai suka dau hanyar dikko ta katsina

****
Kamar yadda suka tsara hakan ce ta kasance sun zaga dangi ko ina sannsn suka koma gombe nsn ma sun zazzaga seda tayi sati daya da kwana uku dan taga kawaye mubarak kuma ya hanata tafiya wai be gaji da ganin ta ba .
 Har seda hamma masdook ya dameta da mita tukuna ta fara daukar haramar komawa kano ta dabo.

Ranar da ta dawo ranar be barta ta huta ba ya dirje ta iya son ransa har seda aka kira assalatu tukuna sannan ya sarara mata ya tafi massalaci.

Rayuwa me dorarwa ce ta kassnce cikin familyn mubarak dikko Allah ya azurta su da yaya da jikoki masu hadin kai da biyaya a tsakanin su ba babba ba yaro ga ilimi daidai gwargwado ka kyauta da kirki.

Matan su mubark ma sun sauka lafiys sun santalo mace da namiji
  Da me sunsn dada da kuma mubarak 2 sun musu takwara a gida daya.
  Duk karshen shekara se an hadu a gidan dada an yi sati sna raha ana capter
 
 Arxiki ya hsbaka ya yalwantu a tattare dasu madook yusuf har shago ya bude na kayan alatu a kano
  Yaran sa biyu yanzu da kuma mace me suna hajara.

  Aisha na da wani cikin a jikin ta dan ahmd ya shekara biyu da rabi
   Ni kiyi ta haifa min yara ko dari ne ni ina so dan sune gatana.

Wannsn taron ma an hallara
Dada ta kalli sama ta godewa Allsh ta kuma godewa Allah da ya bata ikon ganin yayan jikokin ta taga yayan ta taga jikokin ta ga kuma yayan jikokin ta ta gani meya fi mata wannsn dadi ina ma malam na nan ya ga baiwar da Allah ya basu
  Allah abin godiya A kullum nakan ji dadi in har na waiwaya naga zuri'a ta ba karamin dadi nake ji ba a tattare da ni

  Ku rike junan ku da amana kunji yaran nan ku cigaba da hada kn ku ku cigaba da *zumunci*dan kuwa shi ne jarin ku ko bayan raina nasan zaku riki junan ku gaba daya Allah ubangiji ya sada ni da ku a gidan Alljana
  Amin.
 Ta fashe da kuka suka yi kanta gaba daya jikokin nata suka rungume ta.

*****
Bayan sun dawo.gida ne take tsonan shi wai hamma in tambaye ka?
Uhm ina jinki
 Ina budurwar ka zainab?
 Hararta yayi
Ban sani ba
 Hhhhhh wai Allah kai hamma kaso baiwar Allahn nan da yawa
 Ke din ce kin yi min katutu kin hana ni sakat a zuciyata
  Zainab tayi naci tayi tayi amma ta kasa samun kofa har gidan si naji na mata warning na ci mata mutunci dan na gano bibiysta take kuma so take ta wahalar min dake ta shiga tsakanin mu dan ta samu galava Allsh ya fita shi ne fa baban ta yace ta fito da miji cikin sati biyu in ba haka ba ze bata me gardin gidan sa ai seta fashe da kuka tana bani hakuri ta hakura zancen da nake miki ma yanzu ta yi aure kuma yayan ta biyu dan yan biyu ta haifa duk maza kyawawa baki gan su ba kuwa
  Kaje kennsn eh ina zuwa dan abokina take aure
 Kai hamma kwakwa kai ka hada su kennan?
Uhm kinga ko na samu lada
 Gaskiya kam kq samu dama ina wata zee ina kai ai da matsala
 Ban san kuri yarinya kin san dai ita ce first love.

   Ai ta hau ruwan cikin sa tana masa duka ta ko ina ahmad ma ya cangalo yan kafafun sa ya hau gadon ya taya ta suna dkan sa da hannun sa yana dariya yaga abun wasa
  Masdook kam dariya yake tayi yi hakuri wasa nake miki only na kinji bari ahmad harda kai kake dukan dada?
 Ashe group dinku daya wadda za a haifa nasan ni za ta biyo muma mu rama
  ALLAH ka daina kira.min sunsn wata nice first and last luv din ka ya hada da ita da dan sa da cikin ya rungume ysna mata wasa an gama swirry an gama.
    Nima nsn nacs muku bisallam
  Nan na kawo karshen littafin *aisha humaira*
Kuskuren da muka yi Allah ya yafe mana.
  Ina fata na nishadantar daku masoyan aisha humaira.
   _so ba yin sa ake ba so yana faruwa ne kawai lokacin da ya so kuma ga wanda yaso a sanda ya so ko wanne so da tsarabar sa dan kina son mutum ba lallsi ki same shi ba Allah me yin yadda ya so ne me juya ala'amuran sa_
   *Allah ubangiji ya hada kowa da gwanin sa kuma miji na gsri me kula da dukksn bukatun ka mata kuma ba auren ba rashin yin biyayyar msta su daure suna biyayya ga mazajen su suna musu abunda zai sa suji dadi har su sa musu albarka banda kace na ce da miji dan yana kawo bakin jini se kuma a fara smun sabani koda kece me gaskiya bashi hakuri wata ran zaki ci ribar zamam taren dan mace aljannar ta na karkashin kafar mijin ta to yar'uwa ya zaki yi wasa da wannan aljannar? Shi zaman soyayya ai zama ne na amana tunda sna son juna se a daure a ci maganin zama tare dama me auren hakuri*
    Daga marubuciyar:-
*Cin fuska*
*Waye nawa?*
*Zumunci*
*Rayuwa ta*
*yar waye?*
*hatsaniyar so*
*yanayi*
*baka yi min adalci ba*
*rukkaya*
*kausar*
*firdausi*
*na amince*
*karshen rigima*
*hilal da ilham*
*so*
*ban yarda ba*
*son maso wani*
*kuskure*
*meye laifina ?*
*abotar mu*
 Se mun hadu a sabon littafi na me sunan
  *A SANADIN KI*
YANA NSN TAFE BADA JIMAWA BA.

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *