Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Friday, December 7, 2018

BAMU DACE DA JUNA BA COMPLETE HAUSA NOVEL

adsense here
BAMU DACE DA JUNA BA COMPLETE HAUSA NOVEL
[09/02 12:01 pm] Sis Ummu Bashir: 🌹 *BA MU DACE DA JUNA BA*🌹

                   🌹

     { *Short and interesting story* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#[email protected]
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *1~5*





*Cike* da tafiyar k'asaita ta fito daga cikin mota, tafiya take tamkar baza ta taka k'asa ba,Sanye take cikin English wears na riga da skirt,tayi rolling d'in k'aramin veil a kanta, ga Kuma sunglass da tasa. Fuskar ta a d'aure yake babu alamun dariya, yayin da driver yayi saurin bin ta a baya d'auke da briefcase d'in ta. Cike da tafiyar k'asaita ta Shiga parlour'n gidan Wanda ya tsaru ta ko'ina, Driver dake Bayan ta ya ajiye mata briefcase akan kujera, tare da cewa"Madam a huta lafiya"

 Ko kallon shi ba tayi ba bare ta amsa mai, dama already ya Riga ya Saba da halin ta, kawai sai ya fita.


 Wata Mata ce Tana da kyau,tana sanye da kayan alfarma ga gold a wuyan ta da hannayen ta, murmushi ta saki ganin y'ar nata tare da cewa"Lovely Daughter welcome back"

Zama tayi a kujera ba tare da tace komai ba, Matar k'arasawa tayi gurin ta idan da sabo to ta saba da Miskilancin y'ar nata, K'wala ma house maid Kira tayi, ko 5 minutes ba'a d'auka ba sai ga House maid d'in cikin rawar jiki tayi kneeling a k'asa,

Matar tace"hurry up and prepare my daughter's favourite food"

Cikin rawar jiki tace"ok ma" ta nufa wani Had'ad'en kitchen.


Kyakyawar budurwan ko ta kwantar da kanta kan kujera tare da lumshe idanun ta, Matar ta kalle ta tace" My daughter *NIHLA* hope you're okay?"

 Wacce aka Kira da NIHLA cikin sweet voice tace"yeah Mom, I'm just tired" ta k'are cikin shagwab'a.


Shafa kanta tayi Mom tace" Sorry Daughter NIHLA, have your lunch first sai kije ki huta"


House maid ce ta shigo tare da sanarwa ta gama prepared d'in komai, mik'ewa tsaye NIHLA tayi ta Isa dining area kamar baza ta taka k'asa ba,



Fried rice ne with coslow sai ferfesun D'awisu, tare da juices kala-kala, house maid ce tayi serving d'in ta, NIHLA tana Fara cin abinci ta fito da shi tare da d'aukar plate d'in abincin gaba d'aya ta juyema house maid d'in a jikin ta.


A fusace tace"you are fired from this house, idiot do you want to kill me?"


Mom ce ta k'araso gurin tana cewa"what happened NIHLA?"

 Tace"Mom gaba d'aya abincin yayi gishiri"

 Cikin massifa Mom ta fara ma house maid fad'a tana cewa zata kashe mata 'Ya, house maid ko ta kasa motsi daga inda take tsabar ta tsorata.



NIHLA ko barin gurin tayi Cox ita bata jure hayaniya, wani bedroom ta Shiga Wanda ya tafi da tunani na tsabar kyau, komai na bedroom d'in orange and lemon green colour ne, tana Shiga ta cire kayan jikin ta tasa bathrobe tare da Shiga toilet, wow toilet d'in ma ya had'u, shi Kuma lemon green and white colour ne, cika bathtub tayi da ruwa tasa  different performs na wanka, sannan ta Shiga, ta jima sosai tana wanka sannan ta fito inda ta nufa dressing mirror Wanda cike yake da kayan shafe-shafe da make-up, lotion ta shafa sannan ta nufa wardrobe inda Kaya suke a jere ta d'auko wani silk d'in doguwar riga white tasa, gashin ta Yana da tsawo sosai ga santsi, da k'yar ta iya d'aure shi da ribbon white colour, lipstick sai eyeliner kawai tasa sannan ta d'auko wayan ta Wanda tunda ta shigo bedroom d'in yake ringing.


Ganin number'n dake Kiran ta yasa ta jefar da wayar tare da kwanciya akan bed, wayar ko sai ringing yake,daga k'arshe offing d'in wayan tayi, sannan ta samu barci ya d'auke ta.



Around 8:00 pm


 NIHLA na Danna system da alama wani aiki take, knocking taji inda aka bud'e k'ofar, Mom ce ta shigo tace" NIHLA your Dad he's back, ki fito"


D'aga kai kawai tayi, Mom ko fita tayi, sai Bayan 5 minutes ta tashi ta nufa parlour'n Dad d'in ta.



Babban mutum ne Yana sanye da medical glass, Yana duba wasu files, shigowa tayi ta zauna a kusa da kujeran da Mom take tare da gaishe shi, sai da ya ajiye files d'in tare da cire medical glass sannan ya amsa tare da cewa"Ya Maganar mu dake akan kawo min mijin da kike so?"



Shiru tayi tana kallon k'asa Dan tana bala'in tsoron mahaifin ta domin baya d'aukar Wasa da raini.

Ganin tayi shiru sai ya daka mata tsawa yace"are you deaf? Kar ki maida ni k'aramin mutum, lokaci yayi da zakiyi aure domin kinyi karatu har kin gama kin Fara aiki, to meye yayi saura Kuma bayan aure, na Baki 2 months ki kawo Wanda kike so but you refused to, me kike nufi ne?"


Cikin rawar murya tace"Dad please ka sake bani lokaci, zanyi k'okari"

 Tsaki yayi yace"wannan shine last time da Zan baki chance, Nan da one week na Baki if not Zan had'a ki da wani"

A rikice ta d'ago kai ta kalle shi, daka mata tsawa yayi yace ta fita, ai ba shiri ta fita da sauri.


Bayan fitar tane Mom ta kalle Dad tace" please ka dinga yin Mata a hankali..."

D'aga mata hannu yayi alamun baya son jin komai.shiru tayi Dan tasan shi baya son maimaita magana.




NIHLA ko na Shiga bedroom ta fad'a kan bed tare da fashewa da kuka mai k'arfi, wayar ta ne yayi ringing ganin aminiyar tace ke Kira yasa ta d'auka, cikin tashin hankali aminiyar ta ke tambayar meke faruwa?


Tsayar da kukan tayi amma hawaye na zuba tace" *HUDA* what's should I do? I'm totally speechless"

 HUDA tace"calm down NIHLA, fad'a min is everything okay?"

 Tace" Akan lokacin da Daddy ya d'iban min ne, gashi time yayi, yanzu one week kawai ya k'ara min if not yace zai had'a ni da wani"hawaye ya zubo mata.


HUDA tace"oh come-on NIHLA, I've already told you that ki amince da *SABIR*, Kinga Yana son ki"

 Cikin fushi tace"please ki daina min maganar wannan d'an iskan, how many times could I told you that I hated him, please kawai ki k'yale ni"



 HUDA shiru tayi Cox tasan idan friend d'in ta tak'i abu to tak'i shi kenan har abada Haka Kuma idan tana son Abu to zata so shi har abada, Haka dai tayi ta bata hak'uri daga k'arshe sukayi sallama.




The following day


Yau NIHLA ta tashi da ciwon Kai ne, Cox jiya da daddare batayi barci ba sai tunanin maganar Dad take domin tasan shi kaifi d'aya ne, baya maimaita magana Kuma idan ya kafe kan Abu to ya kafe kenan.



Da k'yar tayi wanka ta shirya cikin wani Riga navy blue da black skirt but Yana da fad'i, sai veil black, da tasa Akan ta, handbag ta d'auka sai black hill shoe da tasa, ko make-up Ba tayi ba, Cox she's not in the mood.



Fitowa parlour tayi.................













*I'm back again my fan's*🤸🏻‍♀







 *TAKU CE UMMU BASHEER*
[10/02 11:48 am] Sis Ummu Bashir: 🌹 *BA MU DACE DA JUNA BA*🌹

                   🌹

     { *Short and interesting story* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#[email protected]
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *5~10*



  *DEDICATED TO RAHMAT NALELE*



 *Have this page is yours my lovely Aunty Rahmat, Allah ya kare ki daga sharin mak'iyya da mahassada Ameen, Allah ya k'ara basira da hazak'a k'warin ido tare da laushin hannu Ameen, keep the 🔥 fire burning, and more grace to your shining elbows, Ina yin ki, Ina jinki, Ina tare da ke 4ever, one love UMRAH,(UMMU BASHEER & RAHMAT).*

❤ heart you dear❤







 *Fitowa* parlour tayi inda ta tarar da Mom and Dad suna breakfast, k'arasawa tayi ta gaishe su, Wata house maid ce daban tazo tayi serving d'in NIHLA, Dan an kora na jiya akan tayi abinci gishiri yayi yawa, pepper soup ne da chips with plantain, sai tea mai kauri Wanda yaji Ovaltine, sharp-sharp tayi breakfast sannan tayi musu sallama ta fito waje.



Driver na ganin ta yayi saurin taren ta ya karb'a briefcase tare da gaishe ta, as usual Bata answer ba, bud'e mata back seat yayi ta Shiga sannan ya rufe,tare da bud'e front seat ya ajiye briefcase d'in, suka d'auki hanyar office.




Lokacin da ta shigo office gaba d'aya mutanen gurin suka mik'e tsaye suna gaishe ta, d'aga musu hannu kawai tayi ta wuce, sectary d'in tace ta shigo ta ajiye Mata wasu files sannan suka yi magana ta fita, ba tare da wasting of times ba NIHLA ta fara aikin gaban ta.






 Around 2:00pm in the office


NIHLA sai aiki take a system time to time tana duba wasu files, knocking akayi inda ta Danna wani abu alamar mai knocking ya shigo Cox ita bata jure magana.



 Kyakyawan saurayi ne black handsome guy, ya shigo cikin kayan police, sai murmushi yake yin Mata, d'ago Kai tayi Dan ganin Wanda ya shigo ganin *SABIR* ne yasa ta cigaba da aikin ta Bayan taja tsaki.


K'arasawa yayi gaban ta ya zauna a kujeran da ke facing d'in ta yace"my pretty da alama aiki yayi Miki yawa, should I help you?"


 Ko kallon shi ba tayi ba bare yasa ran answer, an d'auki tsawon 5 minutes kafin tayi magana da k'yar tace" idan ka gama magana zaka iya tafiya"


 Gyara zama yayi yace"I'm not done yet, Pretty please you know I loved you, why can't you accept my love for you, ki amince muyi aure kinji mu haifa Kyakyawan Yara" ya k'are da murmushi.


A fusace tace"how many times Ina ce maka bana son ka, why can't you understand ne, duk matan garin Kaduna ka rasa wacce zaka ce kana so sai ni da ka Raina, kaje ko y'an matan ka, ka aura wata a cikin su but not me"


Murmushi yayi yace"pretty yanzu dai fad'a min why do you hated me?"


 Mik'ewa tsaye tayi ta nuna hanyar fita tace" look SABIR just go"

Murmushi yayi yace"I'm going love but Zan zo gida later" ya fita.

Dafe kai tayi ta nufa fridge ta d'auko coke Mai sanyi ta zuba a glass cup tasha, sannan taji ta samu relief.







In the night


Kwance take kawai tana tunani, Mom ce ta shigo bedroom d'in, ganin halin da y'ar ta ke ciki yasa taji tausayin ta, k'arasawa gurin ta tayi tace"daughter ki dinga rage tunani Kar wani ciwon ya same ki"

Zama NIHLA tayi tace"Mom ya za'ayi in rage tunani Bayan kinsan one week kawai Dad ya bani, I'm confused" ta k'are kamar zatayi kuka.

Mom tace" I know what you're going through my daughter, kiyi hak'uri ko SABIR ne ki fitar a matsayin miji"

 Tace"I don't loved him Mom"

 Tace"nasan ni daughter but da ace Dad d'in ki ya had'a ki da wani fa, ai gara shi Kinga SABIR d'an aminin mahaifin ki ne, gashi can yanzu SABIR d'in a guest room Yana jiran ki"


 Turo baki tayi tace" ni bana son ganin shi kice I'm sleeping"

Mik'ewa Mom tayi tace"no ba za'ayi Haka ba, ki shirya yanzu kizo ki same shi" ta bar bedroom d'in.





 Da k'yar ta shirya cikin wani doguwar riga maroon colour na Swiss lace, wayyo fan's tayi kyau sosai, veil white ta yi rolling a kanta sannan ta fita.


Lokacin da yaga shigowan pretty d'in shi suman zaune yayi Cox ta had'u over, fuskar ta a d'aure ta zauna a kujera, yayin da House maid ta kawo juices and cupcakes.



An d'auki tsawon 10 minutes ba abin da sukace sai sannan SABIR yayi magana but ko kula shi batayi ba har ya gaji da surutun shi ya tafi, sannan ta Shiga bedroom ta d'auki phone d'in ta tana charting da HUDA, inda take sanar da ita abin dake faruwa ita Kuma tana Bata hak'uri.









 *KANO STATE*





 Wani Kyakyawan saurayi ne Wanda ba zai wuce  shekaru ashirin da hud'u ba, sanye yake cikin riga red da jeans black, fari ne mai kyaun jiki irin mazan Nan ne k'arfafa, Yana da tsawo dai-dai, hancin shi siriri, fuskar shi d'auke da saje, Wanda ya fito da ainihin kyaun shi, Kyakyawan saurayi ne Wanda ke tashi yanzu, wani gidan k'asa ya Shiga tare da sallama.



Wata mata dake zaune akan kujera tana tuk'a tuwo,ta amsa,

Da Sauri ya k'arasa gurin ya karb'a mujiyan Yana cewa cikin murya mai dad'i" Umma na, ki Bari inyi" ya karb'a ya fara t'ukawa, yayin da tace" *JAMAAL* baka gajiya ne Kai da ka fito daga makaranta"


 Murmushi yayi Wanda yayi bala'in kyau yace"Meyasa Zan gaji da aikin Umma na? In dai kece Umma na to bazan tab'a gajiya ba"

Murmushi tayi tana sa mai albarka.


Wata budurwa ce ta shigo gidan chocolate colour ce tana da kyau dai-dai gwargwado, tana shigowa ta tuntsire da dariya tace"Umma'n mu, kina kallon Ya JAMAAL sai fasa Miki tukunya? Waya yaga namiji da tuk'a tuwo" ta tuntsire da dariya.


Umma tace" neman albarka yake ai"

 JAMAAL ko dariya yayi yace"yauwa Umma na ni kad'ai, " kinji kunya *RAUDAH* Umma ta fad'i gaskiya"


Wacce aka Kira da RAUDAH d'aure fuska tayi tace"Umma kin gan shi ko"

 Umma dariya tayi tace"Kai idan ka gama bamu guri nida y'a ta"

Ai ko RAUDAH dariya tayi sosai, shi Kuma ya d'aure fuska ya mik'e tsaye yace"to ai sai ki k'arasa t'ukawa"

Zaro ido tayi dan ba abin da RAUDAH ta tsana irin aiki,bare kuma tuk'a tuwo, D'akin shi ya nufa, inda Umma ke dariya wato shima ya Rama kenan.


RAUDAH ko da sauri ta shararo k'arya Wai dama Aiken ta Maman ta tayi sai ta shigo gidan.


Umma ko ta gano ta dariya tayi tace ta tafi, sannan ta k'arasa tuk'a tuwon ta kwashe.




 *TAKU CE UMMU BASHEER (UMRAH)*
[26/02 12:27 pm] Sis Ummu Bashir: 🌹 *BA MU DACE DA JUNA BA*🌹

                   🌹

     { *Short and interesting story* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#[email protected]
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *10~15*




 *DEDICATED TO AISHA ALI GARKUWA*


  *Aunty Garkuwa wannan shafin naki ne, Ina yinki kamar yanda kikeyi na, Ina tare da ke a Koda yaushe tare da Miki fatan alkhairi, Allah ya raya su Basheer da Aysha mu ga Auren su,😍 Allah ya k'ara zumunci da k'aunar juna, ke d'in ta daban ce, ni UMMU BASHEER Ina yin ki sosai, Love you🍇 Allah ya k'ara basira da hazak'a Ameen*

  *Karki damu ana mugun tare irin sosai d'in nan*🍇








 *NIHLA* zaune take a office aiki yayi Mata yawa sai danne-danne take a system, sectary d'in tace ta shigo tana sanar Mata an taru ana jiran ta domin fara meeting.

Hannu ta d'aga alamar taji kawai, sai after 5 minutes ta Isa gurin meeting d'in, tana Shiga duk suka mik'e tsaye, sai da ta zauna sannan suka zauna inda suka fara gudanar da meeting d'in.


 Bayan sun tashi meeting ne ta Shiga office take ganin 5 missed call, duk SABIR ne ya Kira ta, haushi duk ya cikata, ta zauna kenan ya k'ara Kiran ta, a fusace ta d'auki phone d'in.

Da sauri yace"luv hope you're okay? I called you but you didn't answer"

A fusace tace"wai Mai yasa ka cika takura ne? Please leave me alone, I've already told you bana son ka, then ka rabu da ni"

 Jikin SABIR yayi sanyi yace"I'm sorry luv, I don't meant to hurt you"

  Tsaki tayi tare da offing d'in wayan, SABIR ko bai ji dad'i ba.




 Da missalin k'arfe 5:00 pm

NIHLA ce a kitchen sai shirya dinner suke ita da Mom domin ba kowani times ne house maid ke musu ba, Yam balls and chicken souce sukayi with Pineapple juice, daga Nan sukayi fruit salad,Dan kullum sai sunci fruit salad sannan suke cin abinci, domin hakan nada kyau Yana k'ara lafiya.


Bayan sun gama ne house maid ta shirya komai a dining table Sannan NIHLA ta wuce bedroom d'in ta, inda tayi wanka ta shirya cikin riga da wando pink and blue na Pakistan ko veil d'in Bata d'aura ba sai parking gashin ta tayi kawai, earpiece tasa a kunnen ta inda take sauraren music.


Garden ta nufa tare da kwanciya akan grass carpet ta lumshe idanun ta, ba ita tabar gurin ba sai da aka Kira sallan magriba, toilet ta shiga tayi alwala sannan ta fito ta d'aura veil d'in kayan dake jikin ta tayi sallah, a cewar ta baza ta iya saka hijab ba Yana sata Jin zufa.


 Bayan Dad ya dawo aiki ne suka had'u sukayi dinner sannan NIHLA tayi musu sallama ta wuce bedroom d'in ta, sai Bayan tayi aiki a system sai ta kashe wuta tare da barin bedside lamp, tayi barci.








 SABIR Koda yaushe Yana cikin Kiran NIHLA da zuwa gidan su Amma hakan bai sa ta bashi fuska ba sai ma ta gaya Mai bak'aken maganganu, yanzu lokacin da Dad ya bata ya cika gashi Kuma bata samu Wanda take so ba, ita Bata son yin auren ma at all. Lokacin da Mom ta Kira ta cewa mahaifin ta na Kiran ta sai da cikin ta ya murd'a tsabar tsoro, daurewa kawai tayi ta nufa parlour'n shi.



 Tana Shiga ta gaishe shi, sannan ya gyara medical glass d'in shi yace"kinsan dai lokacin da na d'iban miki yayi ko?"

Cikin rawar murya tace"ehm..yayi ....lokacin Dad"


 Yace"then ya maganar mu?" Akwai wani da Kika tsayar a matsayin miji?"


 Tasan mahaifin ta kaifi d'aya ne shiyasa gaban ta ya fad'i tace"Dad kayi min hak'uri Dan Allah wallahi banda Wanda zan tsayar,Amma ka bani lokaci dan Allah"

 A fusace ya mik'e ya mik'e tsaye yace"ni zaki maida k'aramin mutum? Ke har kin Isa tsabar rashin kunyar ki kice in baki time, are you out of your sense?"


Mom ce tace"Kayi hak'uri amma ni Ina......."

Katse mata maganar ta yayi ta hanyar d'aga hannu yace"this is stupidity, duk kece Kika b'ata yarinyan nan, komai take yi da sanin ki, dan haka bazan yi tolerating ba" ya bar parlour'n cikin fushi.


NIHLA fashewa tayi da kuka yayin da Mom ta rungume ta tana rarrashin ta.



Cikin kwana biyu hankalin NIHLA a tashe yake domin bata san wani irin hukunci Dad zai yanke mata ba, HUDA ce mai Mata nasiha da ban hak'uri, gashi SABIR ya nace Mata kamar maye a cewar ta.


Sanye take da English wears na gown maroon colour, tayi rolling d'in veil a kanta ga sunglass da tasa duk ya rufe rabin fuskar ta, light make-up kawai tayi, dawowan ta kenan daga aiki ta shigo gidan.




 Tana Shiga parlour taji muryan mutane a parlour'n Dad, d'aga kafad'un ta tayi irin she don't care, Mom na ganin ta tace tayi lunch Dad nason ganin ta kafin Nan guests d'in shi sun tafi.



Bayan tayi lunch ne ta nufa parlour'n, ba kowa a parlour'n sai Dad, abin da ya bata mamaki shine ganin su goro da sweety, dayawa, gaishe shi tayi sannan tayi shiru.


 Parlour'n ya d'auki shiru tsawon 5 minutes sannan Dad yayi gyaran murya yace"I know you'll be surprised, tunda na baki time ki fito da miji amma kin kasa to shine ni na zab'a Miki miji, D'an Aminina ALHAJI MUSTAPHA, wato SABIR, a yau ne aka sa ranar d'aurin auren ku Nan da 2 months!"



 Tunda ya fara magana take zufa duk da sanyin A.C dake parlour'n, gaba d'aya ta rikice ta rasa mai za tace, she's totally out of her sense, da k'yar cikin rud'ewa tace"Dad kayi min Rai ka taimake ni, wallahi bana son SABIR"

Daka mata tsawa yayi yace"shut up, ni zaki fad'a ma Haka, in baki miji kice wai baki so, kina hauka ne after na baki chance but kin k'i kawo miji Kuma inyi Miki miji yanzu and you're telling me nonsense, tashi ki bani guri idiot kawai"


 Da sauri ta bar parlour'n tana kuka, straight bedroom d'in ta, ta shiga ta rufe tare da fashewa da kuka kamar ranta zai fita.







 *ASALIN NIHLA*


 *NIHLA TAHIR* shine cikaken sunan ta, Kyakyawar budurwa ce y'ar kimanin shekaru ashirin da shida, 26yrs, Fara ce doguwa, tana da eyebrows masu kyau ga pink lips d'in ta gwanin ban sha'awa d'an k'arami, idanun ta farare tas.

 Mahaifin ta cikaken d'an kasuwa ne, Yana zuwa k'asa-k'asa yin business, wani zuwa da yayi k'asar Misra anan ne ya had'u da RUKAYYA, mahaifiyar NIHLA, larabawa ne su, inda suka fara soyayya mai k'arfin gaske, iyayen RUKAYYA da k'yar suka yarda akayi auren da sharad'in zai dinga kawo ta, Haka Koh akayi Bayan Auren suka koma Nigeria, lokaci zuwa lokaci Yana Kai ta, sai Bayan sunyi aure da shekaru had'u Allah ya basu haihuwar y'a mace inda taci sunan NIHLA.



 Kasancewar ta y'a d'aya gurin iyayen ta hakan yasa take zuba shagwab'a duk da mahaifin ta baya son yanda Mom ta shagwab'a ta, NIHLA Kyakyawar budurwa ce tayi primary and secondary School d'in ta anan Kaduna, sannan tayi University ta karanci business, Bayan ta gama Dad d'in ta ya malaka Mata d'aya daga cikin company d'in shi, ta fara aiki.



HUDA aminiyar tace tun suna secondary School har zuwa University sannan HUDA tayi aure, yanzu Haka tana da ciki, HUDA tana da kirki sosai,ita ma y'ar masu kud'i ce.



NIHLA ta d'auko wasu halayen mahaifiyar ta na k'in talaka, Bata son talakawa ga ta miskila ce, da k'yar aga murmushin ta bare kuma dariya, Bata son kaya irin su atamfa da shadda tafi son English wears, tafi son Riga da skirt da veil shine irin shigar ta, a rayuwar ta Bata san wahala ba, ba Wai Bata iya aiki bane A'a Bata son yi ne saboda tana da masu Mata, but sometimes ita da Mom suna yin girki,Dan NIHLA ta iya, Haka Kuma ita ke gyara bedroom d'in ta dan it's her privacy, SABIR Yana son ta amma ko k'adan ba ta son shi domin halayen shi na bin Mata da shaye-shaye, duk da kasancewar shi police, Kuma d'an masu kud'i but she doesn't loved him, Dan she hated maza masu neman mata,   wannan shine dalilin da yasa Bata son shi, to gashi yanzu Dad ya had'a su ya kenan za'a k'are?.







 *Back to story*

  *Cigaban labarin*





  NIHLA hankalin ta ba k'aramin tashi yayi ba Haka tasa Mom a gaba da kuka Wai tayi ma Dad magana ita gaskiya bata son SABIR,


 Mom ko tana son y'ar ta, baza ta so bak'in cikin ta ba, Amma ba yanda zatayi Cox Dad kaifi d'aya ne baya magana biyu, Haka dai tayi ta rarrashin ta da bata hak'uri.



 Shiryawa tayi ta Kira driver ya kaita gidan HUDA, tana Shiga ta fashe ma HUDA da kuka, hankalin HUDA a tashe take tambayar meke damun ta, da k'yar Bayan taci kuka ta fad'a mata!.


HUDA hankalin ta ya tashi Dan batayi tunanin Dad zai yanke hukuncin Nan ba, gashi kaifi d'aya ne Kuma aminiyar ta Bata son SABIR.


 Juice ta zuba mata a cup ta mik'a mata tace"calm down Friend, everything will be okay"

Karb'a tayi Tasha k'adan ta ajiye tace"Friend Ina cikin rud'ani, I don't know what to do, please help me" wasu hawaye masu zafi suka zubo mata.


HUDA tissue paper ta mik'a mata tace"Addu'a makamin musulmai, Ina son ki dage da addu'oi, da sallan dare Allah ya zab'a Miki abin da yafi alkhairi a gare ki, Inshallah Allah Yana amsa addu'oin bayin shi"


 NIHLA share hawayen ta tayi tace"I'm very happy to have friend like you, nagode sosai Kuma Inshallah Zan yi yanda Kika ce"


 Tace"Yauwa my friend, yanzu dai tunda kinzo sai ki tashi ki tayani d'aura dinner" ta k'are cikin dariya.



 Tace"Wai this my baby Yana Baki wahala, girkin ma yanzu da k'yar kikeyi" tayi dariya.



Kitchen suka nufa a tare suna hira kamar basu da wani damuwa, Nan sukayi pounded yam, but flour d'in shi, sannan sukayi egusi soup da yaji nama, sai mango juice da suka had'a.





Bayan sun gama su kaci tare sannan NIHLA ta Kira driver yazo ya d'auke ta, har gate HUDA ta raka ta, sai da ta Shiga mota sannan HUDA ta Shiga gida.












 *Irin wa'inan k'awayen ake so masu baki shawara na gari, Allah kayi Mana tsari da mugayen k'awaye.*








*TAKU CE UMMU BASHEER UMRAH*
[26/02 12:27 pm] Sis Ummu Bashir: 🌹 *BA MU DACE DA JUNA BA*🌹

                   🌹

     { *Short and interesting story* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#[email protected]
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *15~20*



  *Assalamu Alaikum masoyana Ina mai baku hak'urin cewa Zan dakata da rubuta novel d'in DANA SANI...., Saboda wasu dalilai nawa,but Inshallah idan na gama wannan zanyi k'okari in cigaba da yin muku, Ina mai baku hak'uri massoyana,fatan alkhairi gare ku*






 *Dedicated to sis Maimounath & Badeeyerh beuty queen, K'awas*



 *Ina matuk'ar ji ku a raina Ina son ku kamar yanda Kuke Sona, ku sani mu d'in Aminan juna ne, Allah ya k'ara muku basira hazak'a k'warin ido tare da laushin hannu Ameen, Allah ya kare ku daga sharin mak'iyya da mahassada Ameen*


 *Heart you my Sis & K'awas*❤










 *KANO STATE*


 *JAMAAL* na gani sanye cikin riga navy blue and white jeans yayi kyau sosai, sai murmushi yake lokacin da yaga fitowan RAUDAH, ita ko hararan shi tayi tace"kayi dariyan mugunta da kyau tunda ka buge ni"


 Gyara tsayuwa yayi yace"ai that's why nazo baki hak'uri, Cox nasan nayi laifi  I deserve anything"

 B'ata fuskar ta tayi tace"Bayan yau na iya hada amma sai da ka buge ni"


 Yace"surutun ki yayi yawa da y'an aji, ki daina kula su idan sunayi"

 Tace"ba wani Nan sai na fad'a ma Umma na" Nan ta shige cikin gidan su da sauri, bin Bayan ta yayi.



 Tana Shiga ta fara fad'a ma Umma ai yau ya buge ta a islamiyya,Dan tayi surutu kawai, Umma ko fad'a tayi Mai, shi Koh sai hak'uri yake bayarwa.





 Shin wane ne JAMAAL?



 *JAMAAL* Kyakyawan saurayi ne yaro d'an kimanin shekaru ashirin da hud'u 24, sunan mahaifin shi Malam IBRAHIM, mutum ne Mai kirki da son addini, ya kasance talaka ne, Yana da Mata MARYAM (Umma) suna da Yara guda biyu, *JAMEELA* daga ita sai JAMAAL, iyayen su sun basu tarbiyya Mai kyau, Aunty JAMEELA, a yanzu haka tayi aure harda yara biyu *IMAN da AMAN*, mijin da take aure Yana da d'an rufin asiri Haka Kuma tana da kirki, tana son K'anin ta JAMAAL shima yana son Aunty'n shi, Yana da son yara Sosai, shiyasa Koda yaushe Yana mak'ale dasu Iman da Aman, mahaifiyar su tana da kirki ga tsafta da iya girki, sannan akwai ta da son kud'i Dan indai kina da kud'i to shikenan zaku k'ula da ita.




JAMAAL Yana matuk'ar ji da mahaifiyar shi, shiyasa yake Kiran ta da Umma na, baya son ganin tana aiki, Yana kula da ita, Kuma baya son b'acin ran ta, Yana son farin cikin ta, duk da basu da hali sosai Amma suna cin abinci mai kyau, wani lokacin da nama ko kifi, sai dai Umma tafi yin tuwo, JAMAAL Yana da Kaka, wato mahaifiyar Abba mahaifin shi, anan gidan take zaune, akwai ta da ban dariya, sau dayawa tafi Zama a d'aki, a cewar ta Kar ta damu surukar nata, Dan zaman mutunci suke, sai dai Kaka ta rik'e girman ta, Bata cika shigar harkar ta ba, sai idan ana tare da jikokin ne.



Gidan su Yana da d'an kyau duk da kasancewar na k'asa ne, akwai tsakar gida babba,da bishiyoyi guda biyu Wanda ke bada iska, Akwai Parlour da bedroom biyu, Wanda nasu Umma ne, sannan Kitchen a waje,daga can gefe, Ban d'aki ne, da na wanka sai daga can gefe d'akin Kaka ce, sannan ta d'ayan gefen an gaba da na Umma shine na JAMAAL, babban d'aki ne sosai, an shimfid'a carpet blue, sai babban katifa, Wanda akayi shimfid'ar Bedsheet blue da blanket blue, sai wardrobe da gurin sa takalma, da labulaye(Curtains), Suma duk blue ne, sai TV stand Wanda akwai K'aramin plasma, sai decoder na Go TV, d'akin kullum cikin k'amshi yake, ga tsafta, duk da d'akin ba'a zuba dukiya ba,Amma fa ya had'u sosai.




JAMAAL yayi primary and secondary School d'in shi inda ya nufa University na B.U.K, duk da taimakon Aunty'n shi Jameela, kasancewar Allah ya bashi k'wakwalwa Yana da k'okari sosai gashi yanzu har ya gama, inda ya karanci, Building and engineering, sai dai lokacin da ya gama bai samu aiki ba, Dan yanzu aiki sai mutum nada hanya, to gashi Nan dai Yana zaman jiran aiki, sai dai Yana koyarwa a islamiyya saboda Yana da ilimin addini,ya sauke Al-QUR'AN tun Yana da shekaru goma sha shida, yasan litafan addini, dan haka sai Yana koyarwa a wani islamiyya cikin unguwar su, ana Kuma biyan shi albashi.




JAMAAL Kyakyawan saurayi ne sosai kamar yanda nace muku, sai dai Sam Mata basa gaban shi domin yace soyayya ai shirme ne, wasting of times ne, y'an Mata dayawa suna son shi sai dai baya basu fuska ko k'adan Dan tsoron tunkarar shi suke, duk da Yana da fara'a Amma ba kowa yake sakin ma fuska ba, sai iyayen shi da Kuma Wanda ya sani sosai. Yana da aboki Wanda tare sukayi karatun su daga secondary har University, shima dai bai samu aiki ba, sunan shi *Al-Ameen* Yana da kirki halayen su yazo d'aya da JAMAAL sai dai shi Al-Ameen Yana da son y'an Mata kullum cikin soyayya yake da canza y'an Mata, sai dai fa baya neman mata iya ka kawai yayi soyayya dasu kwana biyu ya canza wata, Yana da yayye maza su uku shine na hud'u.







RAUDAH Kyakyawa ce ba laifi black beauty ce, sai dai ko kwata Bata kai NIHLA kyau ba, ita kad'ai ce gurin iyayen ta, RAUDAH akwai surutun tsiya, wani lokacin rashin kunya, gidan su na kusa da nasu JAMAAL ne, su mak'obta ne, kullum tana cikin Shiga gidan su JAMAAL, sun shak'u sosai da JAMAAL, iyayen ma sun San da Haka, RAUDAH Bata son karatu a rayuwar ta da k'yar tayi j.s.s 3, yanzu shekarar ta goma sha Tara 19yrs, islamiyya ma Bata son zuwa, shiyasa JAMAAL ke dukan ta acan.










 *Wannan kenan*



  *Cigaban labarin*






"Come-on NIHLA ki daure ki shirya muje tare ko Zaki ji sauk'in abin da ke damun ki" Mom ce ke fad'a ma NIHLA Haka.



NIHLA dake kwance cikin blanket ta fito da kanta tace"Mom just go, save journey"


 Tace"No My daughter tare zamu je bikin Nan, two days kawai zamuyi fa, kinsan HAJIYA AMINA tana son ki, kuma tace in zo Mata dake"


Zama tayi tace"okay Mom but kinsan ni bana son Shiga cikin mutane especially Kuma biki, kawai dai zanje ne"Nan ta mik'e tsaye ta fara shirya kayan ta cikin wani traveling bag pink and blue Mai kyau, sannan ta Shiga toilet tayi wanka,Bayan ta fito tasa wani Arabian gown peach colour tayi rolling d'in veil a kanta, light make-up tayi sannan tasa hill shoe white da handbag shima white.



Fitowa tayi parlour janye da Traveling bag, Mom ma ta gama shirin ta har ta fito, driver ne ya shigo ya kwashi kayan zuwa mota, inda Suma suka shiga cikin motar driver ya d'auki hanyar Kano.











Around 5:00pm suka Isa Kano, cikin wani Had'ad'en gida Mai shegen kyau motar ta Shiga, driver yayi parking gurin parking lot, da sauri wata Mata ta fito ita da wasu y'an Mata su biyu.



Welcoming d'in su sukayi yayin da suka shiga cikin gidan, abubuwan motsa Baki aka Shiga kawo musu, NIHLA ko Danna waya kawai take Cox ita fa Bata son Shiga mutane, ni ko nace ko kallon abin da aka kawo Bata yi ba, da kin ganta Kinga masu kud'i.




Nan Y'an matan Nan suka Kai ta bedroom d'in su, sai b'ata fuska take Cox tana ganin bedroom d'in yayi Mata local, duk da ko ya had'u, toilet d'in su da k'yar ta iya Shiga, Dan k'yama take ji, Dan ita daga gidan su sai na HUDA take sakewa, Bayan ta fito ma abincin k'adan taci ta kwanta.










HAJIYA AMINA K'awar Mom ce, ita tana zaune ne a Kano,tana da Yara Mata, to shine d'ayan zatayi aure shine tayi inviting d'in Mom da NIHLA.


Ranar mother's day


NIHLA Kam kwanciya tayi a gida tace baza ta je ba, Cox Bata son hayaniyar mutane duk an watse an bar ta ita kad'ai, lokacin da ta gaji da kwanciya ta mik'e ta shirya cikin wani material na Mother's day d'in, doguwar Riga ce, milk and golen colour, style d'in yayi kyau shiyasa tasa, tayi rolling d'in veil na kayan a kanta,wow tayi kyau sosai milk handbag da hill shoe tasa sannan tasa sunglass, ga heavy make-up da tayi, phone d'in ta, ta d'auka ta Kira driver ya kaita Restaurant ta d'an Sha Ice cream.




Suna cikin tafiya a hanya sai wata yarinya ta shigo ta gaban su saura k'adan driver ya buge ta, NIHLA kuma yanda ya taka burkin ne ya tsorata ta, parking yayi yayin da NIHLA ta fito cikin motar a fusace ta nufa yarinyan Dan a ganin ta laifin yarinyan ce da sunyi accident.



 Tana zuwa ta d'aga hannu da niyar Marin yarinyan, cak taji an rik'e mata hannu, d'ago da Kai tayi cikin bala'in mamakin wani Mai gangancin ne wannan?.


Idanun su ne ya had'u da na juna, fusge hannun ta tayi cikin zafi. Shin ko kunsan wane ne? JAMAAL ne Wanda ke zaune yazo wucewa shida Al-Ameen, duk abin da ya faru sun gani,Kuma sun San laifin driver ne shiyasa JAMAAL yayi saurin rik'e mata hannu Dan kar ta Mari yarinyan.





Kallon ta yayi yace"Kar kiyi kuskuren Marin yarinyan nan domin laifin ku ne"


A fusace ta nuna shi daga sama zuwa k'asa tace"and who are you to talk to me like that? Kuma har kayi gigin rik'e min hannu?"


 Gyara tsayuwa JAMAAL yayi yace"ni mutum ne Mai son adalci, Kuma ni mutum ne da bana d'aukar rashin gaskiya,domin kin San laifin ku ne"



Tunda take a rayuwar ta ba'a tab'a fad'a mata irin wannan bak'ar maganar ba sai wannan d'an yaron Wanda she's very sure ta girme shi, tace"you don't have manners, kaje gida a baka tarbiyya, I don't have your time little boy"tana fad'in haka ta shige mota driver yaja suka bar gurin.






JAMAAL ko wani irin bak'in ciki ne ya kama shi Jin abin da tace, a fusace yace"wallahi da kin tsaya sai na nuna Miki rashin tarbiyya"


Al-Ameen yace"Kai kazo mu bar gurin Nan, Dan wallahi k'ila ma y'ar wata babba ce a k'asar Nan"




 Tsaki yayi yace"Kai wani irin matsoracin namiji ne? Idan y'ar wani ne then so what? Da ta tsaya sai na koya mata hankali tunda ita Bata da shi"


Al-Ameen ne ya jashi Yana bashi hak'uri su tafi, Shi ko zuciyar shi tafarfasa kawai yake tsabar bak'in cikin maganar NIHLA.






NIHLA ko ice cream d'in da Bata Sha ba kenan domin bak'in cikin abin da d'an K'aramin yaron Nan ya fad'a mata, lokacin da su Amarya suka dawo Mother's day sai zuba Mata surutu suke, komai ba tace ba,daga k'arshe barin gurin tayi, waya sukayi da HUDA tana Bata labarin abin da ya faru, ita ko hak'uri take Bata Cox tasan an tab'o aminiyar ta.





Washegari Bayan an d'aura aure NIHLA da Mom suka koma Kaduna,yayin da NIHLA still tana bak'in cikin abin da ya faru tsakanin ta da JAMAAL.

















*TAKU CE UMMU BASHEER*
[26/02 12:28 pm] Sis Ummu Bashir: 🌹 *BA MU DACE DA JUNA BA*🌹

                   🌹

     { *Short and interesting story* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#[email protected]
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *20~25*




 *Sister AYUSHERT MUH'D, nagode sosai da Dedication, Naji dad'i ba k'adan ba, yanda kikayi min Sadaukarwa na page d'in KAINUWA, gaskiya I'm very happy Allah ya k'ara zumunci, Allah yasa ki gama novel d'in ki lafiya kamar yanda Kika Fara lafiya, sosai nake Jin ki a raina, ke d'in ta daban ce, Thanks a lot*🕊

🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊







*NIHLA* zaune take a office, gaba d'aya yau ta kasa yin aiki, tayi zurfi a cikin tunani, abubuwa sunyi mata yawa, ga bak'in cikin had'a auren ta da SABIR da za'ayi, wasu hawaye ne masu zafi suka zubo mata, Kai gaskiya Ina baza ta iya yarda a had'a auren ta da SABIR ba.


Mik'ewa tayi tare da d'aukar handbag ta fita a office d'in, driver dake zaune daga can gefe ya taso da sauri Yana cewa"Madam lafiya?, Gida Zan Kai ki?"


Ko kallon shi ba tayi ba ta shige mota, ai da sauri ya Shiga suka d'auki hanyar gida, suna Isa gate man ya bud'e gate, driver ya nufa gurin parking lot yayi parking.


NIHLA fitowa tayi ta Shiga parlour, Mom dake kallon news da sauri ta fara tambayar lafiya ta dawo gida lokacin aiki?, K'arasawa NIHLA tayi jikin ta, tare da fashewa da kuka mai k'arfi.



 A rikice Mom tace"Meya faru ne my daughter?, oya tell me,kinsan bana son kukan ki"


Cikin kuka tace"Mom I swear bana son SABIR, gaskiya ni bazan aure shi ba"



 Mom tace"oh my God, NIHLA please kiyi hak'uri da abin da mahaifin ki yace, kinsan baya maimaita magana, but don't worry inshallah Zan k'ara mai magana"


  Tace"Please Mom help me, Bana son auren Nan, na tsani SABIR, *BAMU DACE DA JUNA BA*"


 Kwantar da kanta tayi a jikin Mom yayin da ita take rarrashin ta har ta hak'ura ta Shiga bedroom Dan baza ta iya aiki a ranar ba.






Around 8:00 pm in the night



Mom ce ta shigo bedroom d'in NIHLA inda ta same ta suna waya da HUDA, tana ganin ta sukayi sallama da HUDA tayi offing phone d'in.


Zama Mom tayi tace"NIHLA get ready kije ki sama SABIR a parlour yazo, and bana son Jin wani magana just ki bar komai a hannu na"


Shiru tayi yayin da Mom ta fita, night gown ne a jikin ta kawai sai ta d'auki After dress ta d'aura akai sai veil, Dan tace baza tayi mai kwaliyya ba.



Zaune ta ganshi a parlour already an kawo mai Juice and cupcakes, ba tare da tace komai ba ta zauna a d'ayan kujeran dake facing d'in shi,


Murmushi yayi yace"my Love hope kina lafiya?"

Hararan shi tayi tace"idan da bani da lafiya will you see me here?"


Murmushi yayi yace"I knew lafiyan ki k'alau ma, I'm very happy you're going to be my wife in the next one month"


 Wani irin bak'in ciki ne taji kamar zatayi kuka tace"ni a matsayin matar ka? I will never be your wife so stop dreaming"

 Yace"haba my wife to be kinsan da cewa Ina mutuwar k'aunar ki, ban tab'a san wata y'a mace ba kamar yanda nake k'aunar ki"


 A fusace tace"Ni Kuma ban tab'a tsanan namiji ba kamar yanda na tsane ka, wallahi na tsane ka SABIR, kar kayi gigin yarda a had'a aure na da naka, Dan *BAMU DACE DA JUNA BA*"


 Yace"haba meyasa kike cewa *BAMU DACE DA JUNA BA*, wait meyasa ba Kya so na?"


 Tace" bana son ka saboda halayen ka na shaye-shaye da neman mata, SABIR har cikin zuciya ta nake fad'a maka Haka,why can't you understand my reasons?"


 Yace"NIHLA idan har ban aure ki ba mutuwa zanyi, na rok'e ki Kar kice ba Kya so na"


 A fusace ta d'auki juice wanda ke cikin cup, ta watsa mai a jikin shi! A razane ya mik'e tsaye ya rik'e rigar Wanda yake fari da hannun shi, lokaci d'aya idanun shi sukayi jajazur.



Cikin zafi tace da d'aga murya tace"I hate you SABIR, bana son auren ka, bana son ka, just live me alone, get out of my side"



A fusace ya d'auki car keys with phone d'in shi ya bar parlour'n. Yayin da NIHLA ta zauna a kujera tare da fashewa da kuka mai k'arfi, sosai tayi ta kuka har sai da kanta ya fara ciwo sannan da k'yar ta nufa bedroom d'in ta.





A wannan Daren da k'yar barci b'arawo ya sace ta.






Cikin two weeks, NIHLA ta Shiga tashin hankali duk ta rame, Dan Mom har fad'a sukayi da Dad but yace Bata Isa ta maida shi k'aramin mutum ba aure dole ne babu fashi, shiyasa duk NIHLA ta fita hayyacin ta, ko abinci sai Mom tasa ta a gaba take cin k'adan.



B'angaren SABIR ko bai sake zuwa ba, sai dai ya wakilta abokin shi akan komai na bikin.




An kawo lefe na gani na bugawa a jarida domin ya had'u iya had'uwa, set biyu ne,har da gold da wata waya mai tsada, komai yaji a kayan Masha Allah, Mom ko duk da taji dad'in ganin kayan bare yanda take son y'ar ta, ta auri Mai kud'i to gashi ta samu, but halin da NIHLA ke ciki Yana d'aga mata hankalin ta.




Yayar Mom daga k'asar Misra tazo sunan ta HAJIYA SHUWERH, ita ma Bata ji dad'in ganin yanda NIHLA Bata son Auren ba, mussaman aka d'auko Mai gyaran jiki Wanda sati d'aya ana gyara amarya NIHLA, ga yanda HAJIYA SHUWERH ke gyaran y'ar ta da magungunan Mata Wanda daga can tazo dasu. NIHLA ko da k'yar ake fama da ita, maganin ko HAJIYA SHUWERH tasa ta a gaba take har sai ta shanye tass ko Bata son Sha kuwa, Dan HAJIYA SHUWERH ba Wasa.





Anyi Abubuwa dayawa,domin Mom da abokanan Ango su suka shirya, ranar Wednesday anyi FRUIT DAY, Thursday Mother's day, Friday akayi Arabian night, duk da k'yar NIHLA taje, Haka take ta kuka, mutane ko gani suke kukan rabuwa da iyayen ta take,basu san dawar garin ba.


Ranar Fruit day ko kaca-kaca sukayi fad'a ita da SABIR domin SABIR ya gaji da yanda take nuna mai tsana k'arara, har cewa tayi gara ta mutu da ta aure shi!.






 Ranar Saturday d'aurin aure




Haka HUDA tasa ta a gaba da k'yar ta shirya cikin wani Swiss lace,dark blue, veil d'in da aka d'aura mata Kuma silver colour ne, tare da necklace and earrings and bracelet duk silver ne, anyi Mata heavy make-up duk da Bata so.






Ba k'aramin mamaki nayi ba ganin Abba(mahaifin Jamaal) da Kuma JAMAAL, sanye suke da shadda na Abba sky blue ne sai na JAMAAL white ne, ba K'aramin kyau yayi ba, k'arasawa Abba yayi gurin Dad sukayi musabaha Yana mai Allah ya Sanya alkhairi.


Bayan JAMAAL ya gaishe shi ne, Dad yake cewa"Ikon Allah yanzu wannan shine JAMAAL d'in"



 Dariya Abba yayi yace"Wannan ai d'an ka ne, shiyasa nace yau tare zamu zo maka d'aurin aure da shi"


Murmushi Dad yayi yace"Allah sarki gaskiya nayi matuk'ar murna, yaro na da fatan ka sani?"


Girgiza kai JAMAAL yayi alamar A'a domin shi dai Abba cewa yayi kawai ya shirya zai raka shi gurin d'aurin aure a Kaduna,to bai san komai ba.


Nan Abba ke bada labarin abin da ke tsakanin shi da Dad a gurin lokacin mutane na sauraren su.



Cewa yayi, shekaru ashirin da hud'u da suka wuce matar shi wato Umma ta tashi cikin dare da nak'uda, gashi akwai matsala dole suje hospital, Haka ya rok'a wani mak'obcin su daya taimaka ya kaisu hospital, haka ko akayi ana zuwa hospital aka Shiga da Umma theater room domin haihuwar yazo da matsala,yayin da aka umarce shi da ya kawo kud'i,gashi bashi da ko sisi, Haka ya bar hospital d'in cikin dare, domin ko mak'obcin su daya kawo su bashi da kud'in yace, har safe Abba na yawon neman kud'i Amma bai samu ba, can Yana cikin tafiya a gefen titi yana tunanin halin da ya bar matar shi, Ashe bai sani ba har ya hau kan titi, wata mota ce ta buge shi, duk da Mai motar yaso tsayawa Amma sai da ya buge Abba, Nan take sai jini, mutane suka taro a gurin da sauri mai motar ya fito shida wani mutum suka d'auki Abba suka sashi a cikin mota suka nufa hospital dashi,suna zuwa aka bashi taimakon gagawa to Alhamdulillah bai ji ciwo sosai ba, sai dai ku'jewa da yayi da Kuma suman da yayi sai kan shi ya bugu Amma da sauk'i ba abin da ya samu kan, lokacin da ya farfad'o matar shi kawai ya fara tambaya,Dad shine Wanda ya buge shi,Nan ya fara kwantar Mai da hankali da fad'a mai abin da ya faru. Nan shima yace sai ya tafi yaga halin da matar shi ke ciki, daya kafe kawai sai Dad yace Bari ya kai shi, suna zuwa aka fad'a ma Abba cewa ai anyi Mata aiki an Ciro D'a namiji suka umarce shi da ya biya bills, Dad da kanshi ya biya bills d'in sannan yayi ma Abba alkhairi ya bashi kud'i masu yawa,tare da bashi number'n shi, yace ya Kira shi idan akwai wani Abu, godiya yayi ta Mai sosai Yana gode ma Allah daya had'a shi da mutumin kirki.




Haka har aka sallame Umma sannan Abba ya Kira Dad ya k'ara Mai godiya sosai, tun daga wannan lokacin suke d'an zumunci da yake ba'a gari d'aya suke ba, Dad yazo Kano wani d'aurin aure ne, shine Yana hanyar zuwa gurin Accident d'in ya faru, lokaci zuwa lokaci su kan had'u har Dad yayi ma Abba alkhairi Wanda kullum sai Abba yace shi Koh da Mai zai saka ma Dad ne? Domin alkhairin shi,




To yanzu ma mussaman Dad yasa driver da ya kai ma Abba invitation card, har Kano, ba k'aramin farin ciki yayi ba shine yace zai tafi tare da JAMAAL domin ya San shi. Wannan kenan.



Cigaba


JAMAAL sauke ajiyar zuciya yayi domin ko ya tuna wani lokacin Abba na bashi labarin, Ashe dai Shine wannan mutumin. Gurin ko sai farin ciki suke, suna cewa ai k'adan daga cikin alkhairin Dad kenan.








Da missalin k'arfe 2:00 pm



Mutane duk an hallara sai jiran Ango ake da iyayen shi Amma shiru ba ko d'aya da yazo gashi d'aurin auren 1:00pm ne za'ayi but har 2:30pm yayi Amma shiru,can dai wani Aminin Dad ya Kira mahaifin SABIR Yana tambayar shi lafiya basu iso gurin d'aurin auren ba, Nan Mahaifin SABIR ke sanar musu cewa SABIR ya fasa auren NIHLA! Domin Bata son shi! Ba k'aramin girgiza kowa yayi ba, Dad ko wani irin azababben tari ne yazo Mai Wanda sai da ya kusa d'auke Mai numfashi!



 Aminin bai gaskata ba sai da ya k'ara Kiran SABIR yaji daga bakin shi, SABIR ko bai b'oye musu komai ba ya fad'a musu irin rigiman da sukeyi da NIHLA Dan Haka shi ya hak'ura domin ba zai auri macen da Bata k'aunar shi ba, da yake a handsfree Aminin Dad yasa kowa na gurin naji,Dad ko yafi kowa Shiga tashin hankali wannan wani irin tozarci ne NIHLA taja Mai, cikin mutane sai kawai ya fashe da kuka mai tsananin gaske, ba abin mamaki bane domin sun San akwai zafi, a fasa auren y'ar ka cikin mutane Bayan an shirya d'aura auren.




Share hawayen shi Dad  yayi ya kalle Abba yace"Ina son idan ka yarda a d'aura auren y'a ta NIHLA da D'an ka JAMAAL!"



Babu Wanda basu razana ba a gurin, bare kuma JAMAAL suman zaune yayi! Cikin rud'ewa da tashin hankali Abba yace"JAMAAL ai yaro ne k'arami, Amma babu abin da zaka nema daga guri na in k'i amincewa"


Dad yace"sai dai idan zaka k'i amincewa, Amma tunda Naga yaron ka naji ya kwanta min a rai naji k'aunar shi lokaci d'aya, Ina rok'on ka, daka share min hawaye na,domin sani cikin farin ciki yanzu"



Gaba d'aya mutanen gurin suka Fara ba Abba hak'uri da ya amince, Abba ko a zuciyar shi cewa yake ya Zama dole ya amince domin Dad ya taimake shi lokacin da yake tsananin buk'atar taimako, sannan ya rasa da Mai zai saka Mai, to yau ga ranar sakayar yazo, shine ya amince bare kuma yanda manyan mutanen gurin ke faman rok'on shi da bashi hak'uri, Nan take yace"wallahi na amince! Ni na ba JAMAAL Auren y'ar ka NIHLA!"


Gaba d'aya gurin akayi kabbara, Dad wani irin farin ciki ne ya ziyarce shi, yayin da JAMAAL kalaman mahaifin shi suka girgiza shi!


Dad ya kalle JAMAAL yace"D'a na ka amince zaka aura y'a ta NIHLA!"


 Wani irin zufa ne yaji ta ko'ina,a zuciyar shi Yana tuna halarcin Dad gare su, bare kuma yanda yake babban mutum har yace shi ya aura y'ar shi Kuma yak'i, lokaci d'aya yaji k'warjinin Dad Nan cikin rawar murya yace"Na amince!"



Habawa ai Nan akayi farin ciki, ba tare da b'ata lokaci ba aka d'aura auren *JAMAAL IBRAHIM da NIHLA TAHIR* akan sadaki mafi daraja Naira dubu Ashirin, Wanda Nan take wani mutum ya biya ma JAMAAL yace shima d'an shine.



Mutane sun shaida wannan d'aurin auren, Masha Allah Nima na shaida, Haka nasan Fan's sun shaida.












*Akwai cakwakiya fa*🙆🏻
















*TAKU CE UMMU BASHEER*
[26/02 12:28 pm] Sis Ummu Bashir: 🌹 *BA MU DACE DA JUNA BA*🌹

                   🌹

     { *Short and interesting story* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#[email protected]
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE *25~30*




 *SAMAREEN BANA*

  *Na Rahmat muh'd Rufa'i Nalele (Aunty luv)*😍



 *Congratulations Aunty Rahmat Nalele Ina taya ki murnan Kamala litafinki da kikayi lafiya, Allah ya k'ara basira hazak'a k'warin ido tare da laushin hannu Ameen, more grace to your shining elbows, keep the fire burning,*

🌹.           🌹.        🌹.    🌹.


 *Ina son ki, Ina jin ki, Ina Bayan ki Ina tare da ke a Koda yaushe,one love keeps us together, ja muje tawan naki ba irin nasu bane, ke d'in ta daban ce Naga yayi gaba na baya sai labari, kin nishad'antar Kuma kin ilimantar damu a cikin litafin ki na SAMAREEN BANA, tsayawa fad'in tsaruwan litafin ba zai fad'u ba a Baki, Amma kinyi bala'in k'okari sosai sister, fatan mu shine Allah ya raba ki da mahassada da mak'iyya, Ameen*

*Kai ku bani guri in d'an taka rawa*💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 *SAMAREEN BANA litafi ne da ya d'auki kusan shekara d'aya ana rubuta shi, karku Bari a baku labari ku nema ku karanta, Amma matan aure kad'ai😜, domin Aunty Rahmat tace Bata yarda kina budurwa ko bazawara ko saurayi ko bazawari, su karanta Mata litafi ba, Nima dai na k'ara fad'a, na matan aure ne irin mu😎 Banda su O'o ehe😏*




*Wayyo hausawa sunce laifin dad'i k'arewa, muna missing d'in SAMAREEN BANA sai mun jiki a sabon litafin ki Mai sunna LIKITAN ZUCIYA, duk da dai kin lasa Mana Zuma a baki😋sai mun jiki*💃🏻










*Dad* ne ya shigo cikin gidan tare da nufan parlour'n shi, Mom na Ganin shi tayi saurin bin Bayan shi Dan taji kamar mutane na fad'in Wai SABIR ya fasa auren, Nan ta fara tambayar shi ko lafiya ya ake ciki?.



Ba tare da b'ata lokaci ba ya sanar da ita komai da ya faru! Ba k'aramin razana tayi ba, domin da ayi auren NIHLA da yaron da yace ai gara SABIR sau dubu a cewar ta, a fusace ta fara magana Tana cewa ai ba zai yuwu ba NIHLA ta aura d'an talakawa,sai dai a kwance auren, Dad ran shi ya matuk'ar b'aci, yace ko Bata Isa ba Kuma yanzu ba sai anjima ba za'a tafi da NIHLA Kano, Kuma babu shi ba ita! Ya cire ta a rayuwar shi!.


Ba k'aramin tashin hankali Mom ta Shiga ba, a fusace ya mik'e ya Isa bedroom d'in NIHLA inda wasu 'Yan uwa'n suke ciki, Yana Shiga yace"Burin ki ya cika na ganin Baki aura SABIR ba, kin wulak'anta ni, kin tozarta ni cikin d'umbin mutane, na had'a ki da miji kin k'i min biyayya sai da Kika sa ya fasa auren"


Jin an fasa auren yasa NIHLA Jin dad'i sai dai maganar da yayi yanzu ya birkita Mata k'wakwalwa, inda yace"To Allah ya taimake ni inda ya bani Wanda zai share min hawaye na, an d'aura auren ki da JAMAAL!Kuma yanzu za'a wuce dake, Ina son daga yanzu ki d'auka Baki da iyaye! Kuma ni bani da wata 'YA!"



 Ba NIHLA kad'ai ba gaba d'aya kowa na gurin sun girgiza da maganar shi, Nan ya umarce HAJIYA SHUWERH da 'Yar uwa'n shi da su shirya ta zasu wuce Kano yanzu, Kuma yace Kar Wanda yaje, sai su biyu, sannan Kuma NIHLA Kar ta d'auki komai nata sai Kaya.



Mom ce ta bishi tace ita Sam bata yarda ba, ko kulata bai yi ba, NIHLA kuka kawai take yayin da zuciyarta ke Mata wani irin azababben ciwo, HAJIYA SHUWERH sun shirya Mata kayan ta, HUDA sai kuka take tana rarrashin NIHLA.



Dad sai cewa yake suyi sauri za'a tafi, duk matan gurin sun tausaya ma NIHLA wannan wani irin aure ne Haka? HUDA ce tayi saurin saka Mata phone d'in ta a akwati, NIHLA rungume Mom tayi tana kuka, da k'yar aka raba su, Har parlour'n Dad aka Kai ta, tana Shiga ta rik'e k'afar Dad "Dan Allah ka yafemin, wallahi Na amince da SABIR, bana son auren Nan, kayi min Rai Dad, wallahi bana son shi"


 Wani gigitacen Mari ya Kai Mata sai da jini ya fito ta gefen lips d'in ta, "har ni zaki fad'a ma haka,?to kije kiyi rayuwar da nasan ba Kya so yanzu ne zakiyi hankali kisan duniya, ki d'auka cewa Baki da kowa a duniya sai inda Zaki" Nan ya umarce su da su jata, tana kuka sosai Haka aka sa ta a mota, su HAJIYA SHUWERH suka shiga.



Motoci biyu ne su Abba suna d'ayan motar, zuciyar JAMAAL ko tafasa kawai yake tsabar bak'in ciki, Haka NIHLA tayi ta kuka a hanya, HAJIYA SHUWERH ke faman rarrashin ta da yin Mata nasiha.



Da missalin k'arfe 8:00pm

Suka Isa cikin Kano State, Abba ne yayi ta ma driver kwatance har suka Isa k'ofar gidan su, sannan motocin sukayi parking, mutanen unguwa sai kallon motocin suke, Dan unguwar 'yan k'auye ne, Da sauri JAMAAL ya fita motan, direct gidan su Al-Ameen ya nufa.


 Abba ne ya Shiga gidan Yana sanar da Umma ga bak'i nan, Shigowa sukayi yayin da fuskar NIHLA ke rufe cikin gyale, da k'yar take tafiya.



Shiga sukayi har d'akin Umma, Nan tasa aka kawo musu ruwa, Abba ya aika aka siyo musu nama dasu juices aka ajiye musu, sannan ya Kira Umma d'akin Kaka ya sanar dasu komai dake faruwa, Umma tayi farin ciki Jin cewa y'ar masu kud'i ce, Kaka ma tayi murna wato rabon aure ne yasa su tafiya Ashe, Nan tayi ta addu'a, ko da suka nema JAMAAL sun rasa shi, kawai suka k'yale shi domin sun San Yana buk'atar hutu.




 A cikin Daren Nan Umma tayi ta aiken Yara gidajen dake kusa Dan sanarwa, Aunty JAMEELA mijin ta ya kawo ta, Nan akayi ta shigowa ana ganin Amarya, Aunty Jameela da wata ce suka shiga d'akin JAMAAL suka k'ara gyarawa duk da d'akin ko da yaushe a gyara yake, sannan aka shigar dasu d'akin, lokacin da HAJIYA SHUWERH taga d'akin sai da ta tausaya ma NIHLA sosai,Haka ma 'yar uwa'n Dad, ita dai fuskar ta na rufe Bata son ganin ma inda take.






JAMAAL ko Yana Shiga d'akin Al-Ameen ya fad'a kan katifa tare da rik'e kan shi da hannu biyu, da sauri Al-Ameen ya fara tambayar shi ko lafiya? Da k'yar cikin bak'in ciki ya sanar da shi komai!

Shi dai Al-Ameen yayi farin ciki sosai sai dai ya tausaya ma abokin nashi ganin halin da yake ciki,Haka dai yayi ta mai nasiha sosai, anan JAMAAL ya kwana da k'yar ma yayi barci.


Washegari aka shirya yin taron biki, tunda abin yazo ba shiri, gashi Kuma ranar su HAJIYA SHUWERH zasu koma, Amma Sai anyi taron da su, Lokacin da aka sanar dasu Maman RAUDAH sunyi mamaki sosai, RAUDAH kuka ta kwana tana yi Dan Allah ya jarabce ta da son JAMAAL, bak'in ciki yasa ta kasa Shiga gidan.



 Da k'yar NIHLA ta tashi, Dan kwanciya tayi ta rufa da gyalen ta, sai da HAJIYA SHUWERH ta nuna mata ranta ya b'aci sannan ta yarda ta shirya cikin Swiss lace pink, tayi kyau sosai ba k'adan ba sai dai rufe fuska tayi-tayi, mutane ko sai shigowa kallon ta suke.



Anyi taro sosai inda aka ci aka Sha, sai dai Amarya tak'i fitowa Kuma tak'i yarda aga fuskar ta, Haka aka yi taro aka watse, da yamma Su HAJIYA SHUWERH sukayi Shirin tafiya, sosai sukayi ma NIHLA nasiha, tare da cewa duk Safiya taje ta gaishe da Maman mijin ta da kakan shi Kuma ta dinga kyautata musu, sannan HAJIYA SHUWERH suka yi Mata sallama ai sai lokacin taji wani irin kuka ya zo Mata, cikin rarrashin ta suka tafi,inda driver suka mai dasu.





Da missalin k'arfe 9:00pm


NIHLA dai tana kwance, yanzu har Bata iya kukan sai dai hawaye kawai dake zuba, Aunty JAMEELA ce ta shigo.


 "K'anwa ta akwai abin da kike so?"

 "A'a nagode Aunty"

 "Toh ni Zan wuce gida, Angon ki yanzu zai shigo"

Wani irin bak'in ciki taji Wai Angon ta mtssss"Sai da safe"


 "Yauwa ki kulan min da k'anni na" ta fad'a tare da fita.


Tsaki tayi a ranta cikin zafi, ba'a jima ba sai ga JAMAAL ya shigo gidan, sanye yake cikin shadda blue yayi kyau sai k'amshi yake, d'akin Umma ya Shiga ya gaishe ta, Nan ya tarar da Abba sukayi Mai nasiha sosai har jikin shi yayi sanyi, dama sai da Al-Ameen ya bashi gasashen kaza guda biyu da fresh milk Wai Yana Ango yace Haka zai Shiga d'akin Amarya ai ba zai yuwu ba shine fa ya basu Umma d'aya sannan ya nufa d'akin shi Yana tsaki a ranshi Wai yanzu d'akin ya Zama na su biyu kenan? Gaskiya shi baya son auren Nan hak'uri kawai yayi.


 Shiga yayi da sallama da k'yar ta amsa Mai, d'akin ba haske sosai kawai sai ya kunna d'ayan glop d'in, da sauri ta d'ago kai ganin ko waye.


Idanun su ne ya had'u da na juna, Zaro ido JAMAAL yayi" ke dama kece aka aura min?"

Hararan shi tayi cikin bak'in ciki " kai wace ce KE anan?"

 A fusace yace"ban sani ba, dama Ashe kece aka aura min, da nasan ke ce wallahi bazan Amince ba"

Tace"da Mai yasa ka amince? Marar kunyar yaro kawai"

Zaro ido yayi yace"ke waye yaron?"

Tsaki tayi ta juya tare da kwanciya Dan Bata jure magana Mai tsawo,

Ba k'aramin haushin ta yaji ba, Dan Haka ko kazar ma sawa kawai yayi a d'an wani k'aramin fridge, sannan ya d'auka pillow da bedsheet ya kwanta kan carpet, tana Jin lokacin da ya kashe glop sai taji tsoro Dan yau ne Rana na farko da ta tab'a kwanciya da namiji a d'aki d'aya, shima ta b'angaren shi Haka yake ji.


K'arfe 2:00 am taji motsi, farkawa tayi sai ganin JAMAAL tayi Yana sallah, tab'e baki tayi taci gaba da barcin ta.

 Da asubah ya wuce massalaci, lokacin da ya dawo ya tarar da ita sai barci take, a ranshi cewa wannan kamar Bata damu da sallah ba, ruwa ya d'ebo a cup, kawai ya watsa Mata, A firgice ta tashi bala'i nace Dan ganin yanda ranta yayi bala'in b'aci abin da ba'a tab'a Mata ba kenan a rayuwar ta.

Kallon ta yayi a zuciyar shi yace ashe dai kyakyawa ce sosai Haka, Dan ranar da suka had'u ba wani kallon ta yayi sosai ba,jiya Kuma Dare ne, sai yanzu yaga Kyakyawar fuskar ta.

Mik'ewa tsaye tayi" Kai meye Haka?"

 "Ba Kya sallah ne, kina ji an Kira sai wani barci kike"

Tsaki tayi"sai ka watsa min ruwa? shin ko kasan ni wace ce?"

Tsaki yayi"I don't want to know, kije kiyi sallah" ya Haye katifar tare da jan blanket, da sauri ta sauka tace"meye haka, Wai Kai baka da respect Koh?"

Bud'e fuskar shi yayi yace" ke Kar fa ki manta ni mijin ki ne, Dan Haka bana son raini"


Kamar zatayi kuka wai d'an yaron Nan ne ke fad'a mata magana gaskiya gwara SABIR sau dubu da shi, fita tayi da k'yar ta iya Shiga bayin, tayi alwala sannan ta dawo tayi sallah, tana son kwanciya amma ta kasa Dan Yana kan katifa,


Lokacin da gari ya waye taje ta gaishe da Umma, ita ko sai nan-nan take da ita, sannan taje ta gaishe da Kaka, sosai taji tana k'aunar Kaka Dan ranar tasa dariya.



Dawowa tayi d'akin tana kallon ko'ina Bata san lokacin da ta saki kuka ba, tsabar bak'in ciki Wai ita ce KE rayuwa a irin wannan gidan, sheshek'ar kukan ta ne ya tashe shi barci.


 "Kina damu na fa"

 Share hawayen ta tayi Nan taji motsin Umma ta kawo musu breakfast da sauri ta karb'a, sannan ta bud'e ganin kayan tea da tuwo yasa kamar zatayi amai, rufewa tayi ta aje gefe.



Wanka tayi ta shirya cikin riga da skirt brown colour. Sannan ne taga phone d'in ta, kunawa tayi, lokacin ne JAMAAL ya tashi, ko kallon ta baiyi ba ya fita d'akin.

Nan ta Kira HUDA a waya, tana kuka take fad'a mata inda take rayuwa, gaskiya ita Bata son JAMAAL ta fad'a mata ai wannan yaron ne da ta tab'a Bata labari, yanzu ace kamar ta tana rayuwa a irin gidan nan Kuma Wai Dad ya aura Mata k'aramin yaro Dan ta girma JAMAAL 2yrs ta bashi, Amma ji takeyi kamar ta bashi shekaru masu yawa,kunsan mace da son girma, gashi Kuma ta had'u da Wanda baya son raini, Dan bazai girmama ta ba. HUDA hak'uri kawai take Bata tana cewa tayi ma mahaifin ta biyayya a Haka sukayi sallama.







For comments 07030865952


*TAKU CE UMMU BASHEER*
[26/02 12:28 pm] Sis Ummu Bashir: 🌹 *BA MU DACE DA JUNA BA*🌹

                   🌹

     { *Short and interesting story* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#[email protected]
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE 30~35*




 *DEDICATED TO REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*


Mrs Hamisu taura(sisin mama (
Ummie Garkuwa
Faty Axland
Hafsat Musa(indon k'auye)
Sadnaf
Meerah
Ayshkhair
Aunty Khady
MSB
Mommy'n sultan
Sweery
Lady Fulani
First lady
Zee yabour
Mommy'n mussadiq
Fashuna
Maman Muhammed
Dee
Biebie Dee
Ummyn yusra
Rafee'at
Fk fannah


 *Ina son ku irin dayawan nan, tsayawa fad'in sunayen ku zai sa mu cinye lokacin but ku sani Ina k'aunar ku sosai Allah ya k'ara zumunci da k'aunar junan mu, pure tana haskawa,*😍


 *Nishad'i da kike samu UMMIE GARKUWA muna matuk'ar jin dad'i sosai, gaskiya kina sani dariya sosai,wacce Bata San ki ba sai ta kusa kuka mu Kam sai dai dariya, Aunty Maryam tace Ummie Garkuwa Bomb😜,oho ni dai ba ruwana ba ni na fad'a ba😎*


*UMMIE GARKUWA Ina yinki Ina jinki Ina tare dake,Ina matuk'ar son ki kamar y'ar uwa ta na jini,💋 gaskiya kina sani nishad'i sosai, heart you dear❤*





*Ban manta dake ba Aminiyar k'warai REAL MAI DAMBU CE,🥗 kina mak'ale a raina Ina mugun yinki, and thanks for the Dedication Allah bar zumunci*😍











*JAMAAL* sanye yake cikin farin yadi Mai kyau milk colour,bai sa hula ba dan shi a rayuwar shi ya tsana hula, shigowa d'akin yayi Yana kallon yanda NIHLA tayi kyau cikin English wears, a gaskiya ta had'u fa, yace a ran shi, ko kallon shi Bata yi ba, ya samu guri ya zauna tare da had'a tea ya fara cin tuwon shi,miyar kuka,yaji dadawa da manshanu. Yana lura da yanda NIHLA ke b'ata fuskar ta, Bayan ya gama yayi brush sannan ya dawo ya taci abinci.


 Hararan shi tayi" Allah ya kyauta in ci wannan abin"ta nuna tuwo tana b'ata fuskar ta.


Zaro ido yayi"ke abincin Umma'n nawa kike cema haka? Kar kici ki zauna da yunwa non of my business"


 Tsaki tayi ba tace komai ba har ya fita, Around 11:15am taji wani azababben yunwa dole yasa ta had'a tea tasha ba Dan ya bata sha'awa ba.


Da Rana shinkafa da miyar dane-dage aka kawo mata ai ko Bata ci ba, har dare sannan ta tuna da nama da fresh milk ai Nan ta d'auko ta fara ci, sai Bayan sallan Isha'i JAMAAL ya dawo.



Ta shirya cikin wani night gown red colour tayi kyau, tana kwance kan bed rik'e da phone, ba k'aramin kyau tayi Mai ba, ga wani irin k'amshi Mai dad'in gaske.


Yana Shiga straight gurin ta ya nufa ya k'wace phone d'in, a fusace ta kalle shi.

D'aure fuska yayi yace"mene ne kikeyi?"

 "Kai har ka Isa ka tambaye ni, why don't you have manners?"

  "Ke ni sa'ar ki ne? Karki manta ni mijin ki ne"

 A fusace cikin bak'in ciki tace"Allah ya kyauta d'an yaro da Kai kawai, wallahi Kai kasan *BAMU DACE DA JUNA BA*, meye zanyi da Kai"


 "Ai nasan *BAMU DACE DA JUNA BA*, ni badan Abba da mahaifin ki Mai zai sa in aure ki tsohuwa dake"


 "Kai nice tsohuwar?"😦

 "To dake mece ce In ba tsohuwa ba, ni mazanyi dake"


Wasu hawaye ne masu zafi suka zubo Mata"Na tsane ka, wallahi gara ace SABIR na aura da Kai, k'aramin yaro"


Rik'o hannun ta yayi ya had'a a Bayan ta ya matse da k'arfi"wane ne k'aramin yaro, ke baki da kunya ko? Wani d'an iskan kike Kiran min?"


 "Wayyo hannu na, ka sake ni"

K'ara matse hannun yayi yace"ni ba sa'an ki bane, bana son rashin kunya"

Sakin hannun yayi ai ko hararan shi ta dingayi a ranta cewa take Ashe d'an yaron Nan nada k'arfi? Ni ko nace oho Zaki sani Nan gaba😂





 Bayan sati biyu


Cikin sati biyun nan NIHLA ta fuskanci canjin rayuwa sosai Dan ba kamar da data ke gidan su ba, abinci ba irin Wanda take ci ba,Haka ruwa ma, ga inda take rayuwa gaskiya bata son irin rayuwar Nan, Abu d'aya ke Mata dad'i shine idan taje gurin Kaka suna hira, tunda Umma ta lura NIHLA Bata iya cin abincin su, sai tana sa JAMAAL ya siyo Mata irin su take away ko baya so sai ya siya dole, ko ruwa Swan water Umma ke sashi siyowa, Tunda NIHLA ta Gane Umma na son ta sai taji dad'i har tana k'okarin cin abincin duk da sau dayawa idan taci sai zuciyar ta yayi ta tashi kamar zatayi amai, Dan Bata Saba ba, B'angaren ta da JAMAAL ko, kowa na harkar gaban shi Amma duk ranar da wani Abu ya had'a su to zata gaya Mai bak'aken maganganu, shi Kuma ya nuna Mata bai son raini shine gaba da ita, ya matse hannun ta, Kuma hakan ba zai hana ta k'ara Mai rashin kunya ba, kullum cikin waya suke da HUDA tana cewa tayi ma mijin ta biyayya sai tayi banza da ita, sunyi waya da Mom inda take kuka tana fad'a mata irin rayuwar da takeyi Dan Haka Mom tace zatayi tunani ta samo musu solutions Dan Bata son Y'ar ta tayi rayuwar talauci.


 Wata Rana RAUDAH ta shigo gidan kawai sai taci karo da NIHLA a tsakar gida,ba k'aramin tashin hankali ta Shiga ba ganin NIHLA kyakyawa har sai da ta tambaye Umma wace ce shine take fad'a mata matar JAMAAL ce, ta rud'e sosai inda ta koma gida sai kuka take tana bak'in cikin yanda NIHLA ta fita komai, tasan dole JAMAAL yaso NIHLA Kuma dole suyi rayuwar aure Wanda RAUDAH ke bak'in cikin hakan, ni ko nace ai matar shi😒



NIHLA na kwance kan katifa tasa three quarter da K'aramin top tana Shan iska kasancewar ana zafi sosai gashi ta Saba da A.C Nan ko sai celling fan, JAMAAL ne ya shigo dawowan shi kenan daga masalaci sallan Isha'i, kusan suman tsaye yayi da ya ganta.


K'arasowa yayi kusa da ita ai bai san lokacin da ya kwanta kan katifar ba tare da rungume ta, a firgice ta juyo sai ganin JAMAAL tayi, ture shi tayi tace"Kai wani irin iskanci ne Haka?"

 Lokacin da idanun shi suka Kai kan breast d'in ta duk sai ya rikice, habawa ai bai san lokacin da ya had'a bakin su ba Yana Mata wani irin kisses, tunda suke a rayuwar su basu tab'a Shiga irin yanayin Nan ba, NIHLA jikin ta rawa ya fara, gaba d'aya ta manta a wani duniyar suke, nace duniyar luv😂


Da k'yar ta iya ture shi, tana goge bakin ta da hannu, shi ko sai sauke ajiyar zuciya yake.

 "Yanzu d'an yaro da Kai ka iya iskanci?"

 "K'adan ma Kika gani"😉

  "D'an iska kawai nafi k'arfin ka, da zaka wani had'a baki na da naka,shin ko ka manta ko ni wace ce?"

Tsaki yayi yace"wace ce ke Bayan Mata ta, look nine nafi k'arfin ki, Dan ni saurayi ne ba tsoho ba" ya mik'e ya bar gurin Yana lashe lips d'in shi gaskiya kiss yayi idan har Haka yake da dad'i. Yake fad'a a ran shi.

 Tsaki tayi ta d'auki brush d'in ta taje waje Wai a dole zata goge kiss d'in da yayi mata😆


JAMAAL ko Yana fitowa waje ya had'u da Al-Ameen, shaking hands sukayi, a kunne JAMAAL yace ma Al-Ameen"Kai Aure fa yayi a rayuwa"

Dariya Al-Ameen yayi yace"Kai friend kace kaje duniyar ma'aurata ka dawo?"😂


 "Ban je ba tukun amma na kusa"😉

"Gaskiya Nima ina son yin auren Nan inji Wai me ake ji ne"

 "Kai nifa sai dai in San auren but bana son ta"


"Come-on ka daina cewa Haka, Kar wata Rana kazo kana min kukan love d'in da kake Mata"


 "Mtssss Kai banza ne wani lokacin, Allah ya kyauta inyi kuka akan love, never"


Haka dai sukayi hira k'adan sannan sukayi sallama, lokacin da ya Shiga gida already ya samu har tayi barci, kasancewar rigar da tasa k'arami ne har ana ganin breast d'in ta, kwanciya yayi kusa da ita sai k'are Mata kallo yake, gaskiya duk yanda yake tunanin NIHLA ta wuce Nan, she's very beautiful, Haka ya kwanta kusa da ita har asubah.


Gyara kwanciya tazo yi, kawai taji ta jikin mutum, ihu ta saki da sauri ya had'e bakin su Yana tsotsan lips d'in ta,sai zaro ido take cikin tsoro dan ba haske sosai, Haka yayi ta romancing d'in ta, lokacin da ya Kai lips d'in shi kan nipples d'in ta ai duk sai ya birkice, ita kanta a rud'e take sosai. Knocking d'in k'ofar da akayi ne ya dawo dasu hayyacin su, dan dama kullum Abba Yana tashin JAMAAL Dan kar yayi late.


Cikin sanyin jiki yake sanar da Abba cewa ya tashi, ko da yaje massalaci ya dawo k'ara mak'ale NIHLA yayi, already dama tayi sallah ta koma barci.


Sai da safe ta bud'e ido taga JAMAAL ya wani rungume ta kamar irin za'a gudu da ita d'in Nan, da k'arfi ta buge shi, bud'e ido yayi cikin Jin barci yace"oh baby I'm feeling sleepy"

Ture shi tayi tace"are you out of your sense, Kai meyasa baka da kunya ne, ni sa'ar ka ce"

 "I'm your husband fa,so you should respect me"

Tsaki tayi ta tashi, ta nufa bayi Dan yin wanka,Cox already akwai hot water a flask.


Har ta cire kayan ta ta d'aura bathrobe d'in ta tana son yin brush, kawai sai taga wani k'aton kenkeso, wani irin ihu tayi ta fito a guje.


Umma dasu JAMAAL duk sun fito, ai Bata San lokacin da ta rik'e hannun JAMAAL ba tana pointing d'in bayin.

Umma tace"lafiya mene ne?"

 "Wayyo Allah na cockroach ne"

Dariya JAMAAL ya k'yalk'ale dashi.

Kaka tace"oh ni Jumai mene ne Haka Kuma?"

Umma tace"Wai mene ne ka tsaya kana wani dariya?"

"Wai tsoron kenkeso takeyi"😂

Tafa hannaye Kaka tayi tace"yau naji shirmen banza yo ba sai ka kashe mata shi ba ka tsaya kana dariya"


 "Kaka ita ta kashe Mana"😏

Umma tace"yi hak'uri d'an albarka, je ka kashe shi"

Shiga bayi yayi but bai ga komai ba sai cewa yake kawai dai NIHLA ta cika tsoro ne ba komai, ita ko sai murgud'a Baki take tsabar haushi.


Dole ta Shiga bayin tayi wanka but a tsorace take fa😂











*Janih one love*💘











*UMMU BASHEER CE*
[26/02 12:28 pm] Sis Ummu Bashir: 🌹 *BA MU DACE DA JUNA BA*🌹

                   🌹

     { *Short and interesting story* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#[email protected]
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE 40~45*



 *DEDICATED TO UMMI AISHA*


 *Aunty Aisha wannan shafin naki ne gaba d'ayan shi, thanks for your love and care,Ina mugun yinki a raina, Allah ya k'ara Miki basira da hazak'a k'warin ido tare da laushin hannu a cikin litafin ki na ALWASHI.....!*💍


*Kamar yanda nace Miki ga naki page d'in*😍




 *UMMIE GARKUWA BOMB*😎💋





*Yinin* ranar NIHLA tayi shine a d'aki cikin jin kunyar fitowa Dan tana tsoron kar su Umma su gane, shi ko gogan naku sai wani ririta ta yake Yana tambayar meke damun ta ko kallon shi ba tayi, ba wani kunya a tare da shi sai ma farin ciki.


Umma ce ta lura bata fito ba, shine take tambayar JAMAAL sai yace bata da lafiya ne, kawai sai Umma ta fara murna a tunanin ta ko ciki NIHLA take dashi, Bata san sai yanzu ya cika aiki ba.


 Ferfesun kaji Umma ta shirya ma NIHLA Wanda yayi mugun dad'i, har d'aki ta Kai Mata tasa ta a gaba sai da taci.
 Kaka ma tuwo miyar d'anyar kub'ewa ta kawo Mata,sai wani ji da ita suke.



Kan ta har ciwo yakeyi Dan ba k'aramin wahala JAMAAL ya bata ba, HUDA ce ta Kira ta ai ko NIHLA ta fad'a mata abin da ya faru har tana kuka Wai d'an K'aramin yaro dashi sai iskanci ya iya, Dariya sosai ne ya kama HUDA sai dai tayi shiru tana Bata hak'uri da nuna mata Haka auren yake sai tayi hak'uri. Shigowan JAMAAL d'in ne yasa ta kashe phone d'in.


K'arasawa yayi kusa da ita ya tab'a wuyan ta yace"hope you're feeling better Baby?"

 Tsaki tayi ta ture hannun shi"non of your business, and karka sake Kira na da wani suna baby, Dan na wuce haka"

 Murmushi yayi yace" shikenan ai tunda ba Kya so Dan ma kin samu Ina  Kiran ki da sunan, sai ince Miki Aunty ko?"

"Oho Kai ka sani d'an iska mugu kawai"

Zaro ido yayi "Wai har yanzu ban gama maganin wannan rashin kunyar ba ko?"

 "Kai ne baka da kunya ai"

Rik'o hannun ta yayi da sauri ta fara k'okarin k'wacewa Dan tasan ta Shiga uku idan ta Shiga hannun shi, K'akarfan namiji ne shiyasa ta kasa k'wacewa, kissing d'in wuyan ta ya fara yana blowing Mata iskan bakin shi, tuni ta fita hayyacin ta, gaba d'aya sun fita hayyacin su sai romancing suke can NIHLA ta dawo hayyacin ta, ture shi tayi, da sauri ya rik'o ta tare da kashe wutan d'akin.




After 3 hours

Lokacin da na koma d'akin na hango ta sai kuka take tana cewa Bata yafe Mai ba, shi ko dariya yake kawai, Dan ba k'aramin danbe suka ci ba kafin yayi nasarar samun abin da yake so.daga k'arshe ma k'yale ta yayi Wai Dan taga ma Yana kula ta ne ai.






After 2 weeks



Cikin satin Nan NIHLA ta ga ta kanta, Dan ko JAMAAL baya saurara Mata da danbe yake samun biyan buk'ata.Sosai take wahala har ta fara ramewa saboda yanda ya sata a gaba, yanzu dai ta hak'ura Dan baza ta iya danben ba k'arfin su ba d'aya ba, kawai sai tana k'yale shi, har mamaki yake ganin tayi sanyi yanzu.



Zaune take kan kujera tana taya Umma aiki sai gashi ya shigo tare da RAUDAH tana rik'e da kwano a hannun ta Wai a dole girki tayi ta kawo mai shine suka had'u da zai shigo.


RAUDAH ce ta gaishe da Umma yayin da ta harari NIHLA, ita ma ta kula shiyasa ta tsane ta bare yanzu taga sun shigo tare Nan wani bala'in kishi ya rufe mata ido.


 "Umma'n mu Bari in Taya ki aikin"cewar RAUDAH


 Cikin haushi NIHLA tace"A'a ki barshi ma, ni kad'ai na Isa inyi Mata komai, ko Umma'n mu nida JAMAAL?"

 "Haka ne y'ar albarka, RAUDAH ai Bata son aiki"

Haushi taji da Umma ta gwasale ta,


JAMAAL ne ya karb'a kwanon hannun ta"godiya nake RAUDAH ta, NIHLA ki same ni a d'aki"


RAUDAH taji dad'i ta Kuma ji haushin Kiran NIHLA d'aki da yayi k'ila ma wani abu za suyi a cewar ta,ni ko nace Ina ruwan ki tsakanin Mata da miji sai Allah.


NIHLA ko hararan Bayan shi tayi da ya nufa d'aki, Wai har da cewa RAUDAH'n shi, Kuma har wani girki tayi Mai ai ko baza ta yarda yaci ba, Dan baza ta d'auki wannan rainin na RAUDAH ba.



Umma tace"yi maza ki bi mijin ki Yana Kira"

 Tashi tayi ta Shiga d'akin Bayan ta lura da yanda RAUDAH ke cika tana batsewa,😂



 Kallon ta yayi tare da Mata signal da ido d'aya"looking sexy baby"😉

 Turo baki tayi gaba Dan yanzu ta fara sabawa da iskancin shi. Riga da skirt ne sunyi Mata kyau, maroon colour da touch d'in blue.


 Hijabai ne sun different colours, Dogaye har k'asa yace tasa, wow looking take away, hijab na mugun yin Mata kyau, can ya Ciro nik'ab Wai zai sa Mata, ture shi tayi tace"what do you mean?"

 "Shigar da nake son ki dingayi kenan, hope you get it"

 Zaro ido tayi"gaskiya ni bazan iya sa wannan hijab d'in ba yayi min yawa,Kuma wannan bak'in abin so kake numfashi na ya dinga d'aukewa ban so Allah"

 "Wannan Kuma ya Zama dole kisa ba Wai Ina neman choices d'inki bane, do you understand my........" Ya k'arike Mata a kunne.


Zaro ido tayi ta bud'e baki, cikin mamakin maganar shi, gaskiya JAMAAL ya cika d'an iska.

 Ganin Bata rufe bakin ba sai ya had'a da nashi yayi sucking d'in ta.

Ture shi tayi, Cox she's speechless

D'aukar abincin da RAUDAH tayi, da niyar ci, da sauri ta karb'a tare da ajiyewa, shiru yayi yaga Mai zatayi ai ko ta shayar dashi mamaki Dan romancing d'in shi ta fara sannan aka Lula duniyar ma'aurata, ai ko abincin da bai ciba kenan.




Rayuwa kenan yau Kai ne gobe ba Kai bane, Dan a yanzu NIHLA tayi hak'uri domin yin ma mahaifin ta biyayya a karo na biyu, ta cire duk wani girman Kai da k'in talaka, yanzu tana zuwa islamiyya na matan aure sannan tana yin Haddar Qur'an Wanda JAMAAL ke k'ara Mata, ta dage sosai ta cire Wasa a ranta, yanzu doguwar hijab da nik'ab take sawa,su NIHLA ustaziya😜. Gashi sosai suke shiri da Aunty Jameela Dan akwai kirki, fa Iman Wanda kusan kullum tana gurin NIHLA sun shak'u sosai da yarinyan har tana sha'awan samun haihuwa, yayin da JAMAAL yayi serious akan neman aiki, sai dai Bai samu ba. Gashi yanzu Allah ya jarabce shi da K'aunar NIHLA, sosai yake nuna mata zallan so da k'auna, Wanda har RAUDAH ta gani sosai, taji haushi tayi Kuma niyar sanar dashi abin da ke zuciyar ta Dan ya aure ta.




HUDA ita da mijin ta sun kawo ma NIHLA ziyara, ba k'aramin farin ciki sukayi ba da ganin junan su sai dai HUDA tayi ta kuka ganin inda NIHLA ke rayuwa domin tasan ko ita wace ce,da zasu rabu sai da sukayi kuka.






Wata Rana JAMAAL na karantarwa a islamiyya da yamma sai ga wani Had'ad'en mota yayi parking, wani mutum ne ya fito inda suka gaisa yake cewa, dama ogan shine ya turo shi kan cewa an Samar mishi Admission letter a A broad Canada, zai je ya cigaba da karatu, ba k'aramin girgiza yayi ba,domin yasan bashi da wani da ya sani da sai Samar Mai Admission, Kuma Wai a k'asar waje, Bai yarda ba, sai da mutumin yace ai Abba yasan da maganar sannan ne suka samu Abba a kasuwa inda yake ta murna domin shi dama sunyi magana da ogan mutumin Kuma sun San junan su, yayi farin ciki sosai.

Godiya sukayi ma mutumin ya tafi a cewan zai dawo suyi magana da JAMAAL akan tafiya k'asar wajen domin shine zaiyi Mai komai na tafiya Wanda tafiyar saura wata biyu.



 JAMAAL yayi farin ciki sosai Yana ma Allah godiya,bayan ya koma gida ne yake sanar dasu Umma sunji dad'i sosai Kuma sunyi Mai fatan alkhairi,sai Bayan yayi wanka yaci abinci sannan ya samu NIHLA da maganar.


Riga da wando ne a jikin ta sunyi matuk'ar mata kyau, Zama yayi kusa da ita tare da rik'e hannun ta.

 "Baby I love you so much and I want to spend the rest of my life with you, Ina son ki haifa min Yara masu kama dake, Ada nayi tunanin *BAMU DACE DA JUNA BA* sai yanzu na gane cewa *MUN DACE DA JUNA*, na Aure ki ne saboda in ma iyayen mu biyayya, sai Bayan na aure ki na Gane ko ke wace ce, nasan da cewa kina da taurin Kai da rashin d'aukar raini,Haka ba Kya k'aunar talaka, sai daga baya na gane cewa rashin sanin suwa talakawa yasa Kika tsane su, Mace ko indai tana da kud'i dole tayi girman Kai, sai daga baya na Gane ba Haka kike ba,ke mace ce mai kamun Kai, Mai son mutane, ke mace ce Mai tarbiyya, tabbas kina da tarbiyya Kuma ni na shaida hakan Ina ma Allah godiya da ya bani ke a matsayin mata ta, NIHLA ni JAMAAL Ina k'aunar ki fiye da tunanin ki" ya k'are maganar yana kissing d'in hannun ta.




Tunda NIHLA take a rayuwa ba'a tab'a fad'a Mata irin wannan maganar ba, ko SABIR Bai tab'a yabon ta ba, Bata San meyasa ba ta samu kanta cikin farin ciki sosai sai dai Bata son yayi saurin gano ta sai ta k'wace hannun ta.

 "Please let me sleep"

Murmushi yayi kawai Cox bai ji dad'in yanda tace ba, sai yace"Duk da bana son mu rabu ya Zama dole mu rabu"


A firgice cikin rud'ewa ta katse shi da cewa"Mai kace?"

 Shafa kanta yayi"calm down baby, kina mak'ale a cikin zuciya na"ya d'aura hannun ta saitin zuciyar shi.

Ajiyar zuciya mai k'arfi ta saki "Please explain to me why are you saying all this?"


 "Cox na samu Admission letter" ya rungume ta cikin farin ciki sosai tare da sanar Mata duk abin da ya faru game da tafiyar shi da taimakon shi da akayi.


 Bata San lokacin da ta fashe mai da kuka ba,ta rasa kukan bak'in ciki ne ko na farin ciki "Please don't leave me alone, Don't go away from me, JAMAAL nasan Zamu jima ba muga juna ba, ka sabar min da kwanciya a jikin ka, sannan ka shagwab'a ni, ka koya min ilimin addini yanzu idan ka tafi ya zanyi?"duk a rud'e take maganar.



Rungume ta yayi a jikin shi Yana shafa Bayan ta, trying to calm her down Cox baya son ganin ta cikin wani irin hali.





 Cikin wata d'aya sai shirin tafiya kawai JAMAAL keyi. Ga Kuma tunanin barin matar shi da zaiyi. Zai d'auki tsawon shekaru uku acan kafin ya gama karatu ya dawo, NIHLA kullum cikin tunanin tafiyar shi take,Haka zaiyi ta rarrashin ta da nuna mata ai suna tare zasu dinga waya.mutumin Nan ya gama shirya mai komai saura Wata d'aya ya tafi.



 A cikin kwanakin Nan NIHLA Bata Jin dad'i dauriya kawai take, tana yawan Jin jiri ga kasala, tayi fari ta k'ara kyau ga JAMAAL sai manne mata yake domin wani irin ni'ima ya k'aru a jikin ta,ga breast d'in ta sun ciciko, ni Ummu Basheer Anya NIHLA bata harbu ba kuwa? Ko tayani bincike massoya na.


RAUDAH sai wani yawan shige ma JAMAAL take, shi Kuma Bai San komai ba har ga Allah ya d'auke ta a matsayin K'anwar shi ce, NIHLA ko tana maganin ta domin akwai wani tana da ta shigo musu d'aki ba sallama Wai ta kawo mai abinci, har zai tashi daga kujeran da yake kawai sai NIHLA ta zauna kan cinyar shi ta had'e bakin su tana Mai wani irin kiss mai rikitarwa, dama a matse yake, tuni ya rud'e ya fara romancing d'in ta, ai ba shiri da sauri RAUDAH ta fita d'akin Kar zuciyar ta ya buga saboda kishi, su ko sun ma manta da ita, tun daga nan Bata k'ara Shiga d'akin ba.


















*Janih one love*💘









*UMMU BASHEER CE*


 *For comments only 07030865952*
[26/02 12:28 pm] Sis Ummu Bashir: 🌹 *BA MU DACE DA JUNA BA*🌹

                   🌹

     { *Short and interesting story* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#[email protected]
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE 35~40*




 *Wannan shafin sadaukarwa ne gare ku ban manta da ku ba*

*Real Maman Khadija*
*Na'ikke*



*Sorry fan's ba kullum zaku dinga samun posting na ba, saboda abubuwa da sukayi min yawa yanzu, Ina k'aunar ku*💘


 *Wannan shafin Kuma naku ne, massoya litafin Bamu Dace Da Juna Ba, Ina yinku kamar yanda Kuke yi na, ana mugun tare irin sosai d'in nan*💋



 *UMMIE BOMB*😎





*Shiryawa*  tayi cikin doguwar Riga orange colour, fitted ne yayi mugun Mata kyau sosai, lipstick and eyeliner kawai tasa sannan tayi rolling d'in veil a kanta, phone d'in ta, ta d'auka suka Fara charting da HUDA inda HUDA ke sanar Mata zasu zo da mijin ta next week, ba k'aramin dad'i taji ba kuwa, Nan take fad'a mata irin iskancin JAMAAL tana cewa bashi da kunya, sosai HUDA tayi ta dariya, Dan tasan akwai rigima Nan gaba, Haka sukayi hira then sukayi sallama.

 Fitowa tayi ta tarar da Umma dake k'okarin hura icce gashi iccen sai hayyak'i yake ba Mai kyau bane, NIHLA mamaki take yanda suke rayuwa a hakan sai Kuma taji tausayin Umma ya kamata ta,Nan take ta k'arasa ta karb'a maficin daga hannun Umma tana cewa"Umma kawo inyi"


"A'a 'yar Nan ba'a ayi Haka ba,jeki zauna ke da Baki Saba da irin wannan ba"

 "Umma ba komai" ta karb'a maficin ta fara fifita wutan, lokaci d'aya ta fara hawaye saboda hayyak'i can sai ta fara tarri, JAMAAL ne ya shigo yaji dad'in yanda ta Taya Umma wani abu, Amma Dan taji haushi sai yace"meye ne kike wani tarri daga yin fifita, ai gara ki Saba Dan Nan gidan ba electric Cooker"

Ba k'aramin haushi taji  ba sai dai ta daure Dan kunyar Umma take da sai ta rama.


"Kai gidan ku, 'Yar tawa kake fad'a ma Haka ban son iya shege fa"cewar Umma


"Au Umma na yanzu kin daina Sona kenan, Dan kin samu wannan?"😰

  Kafin tayi magana sai ga RAUDAH ta shigo gidan da sauri tana cewa"Yaya na albishirin ka?"


 Da murmushi ya kalle ta yace"RAUDAH ta goro fari k'al irin Wanda Kaka ke ci"


 "Na iya hadda na yau sosai wallahi"

Dariya yayi yace"wayyo shine kike murna haka sai kace an biya miki aikin hajji"


Hararan shi tayi cikin Wasa, Umma ko dariya tayi yayin da NIHLA take bala'in Jin haushin RAUDAH Cox she hated her.

Kaka ce ta fito tana cewa"naji ance Farin goro na shine nazo a bani"

Dariya sukayi dukan su.




Around 7:00pm


JAMAAL ne ya shigo cikin sallama, amsa Mai tayi a hankali, Zama yayi kusa da ita yace"ki shirya muje gidan Aunty Jameela"

Ok kawai tace tare da d'aukar veil d'in ta tace a shirye take, kallon ta yayi daga sama zuwa k'asa, Riga pink ne da skirt Mai d'an fad'i black, tsaki yayi cikin takaici yace"kina nufin a Haka Zaki fita kamar ba musulma ba?"


 A fusace tace"nice ba musulma ba? Why don't you have manners uhm?"

 Mik'ewa tsaye yayi da sauri taja da baya Amma Ina sai da ya rungume ta very tight tare da had'a lips d'in su ya fara kissing d'in ta in a passionate way, da k'yar ya k'yale ta Bayan ya ga dama.


 "Oya wear your hijab"

 "I don't have"

 "Then ba Zan fita dake a Haka ba"

Nan ya hau bincikar kayan ta sannan ya ga k'aramin hijab shima sallah take da shi.ya wurga Mata yace tasa. Ba'a son ranta tasa ba sai Dan kar ya sake kissing d'in ta.

Iya gwiwan ta ya tsaya Mata, ba Haka JAMAAL yaso ba yaso ya sauka har k'asa, Haka Nan dai sukayi masu Umma sallama suka fito.


Kasancewar akwai farin wata ga hasken wuta a unguwar shiyasa mutane keta faman kallon NIHLA wacce hasken fatar ta ya k'ara fitowa ga wani irin kyau da tayi, maza sai kallon ta suke, yayin da ya rik'e hannun ta tsabar bak'in cikin yanda maza ke kallon Mai Mata, Anya JAMAAL ba kishi kake ba kuwa😂



Gida ne d'an madaidaici Mai kyau, nan suka shiga cikin sallama. Yaran tane suka rungume JAMAAL cikin farin cikin ganin shi, Sai d'aukar su yake Yana musu Wasa cikin so da k'auna, Aunty Jameela ce ta fito tana welcoming d'in su.


Zama sukayi a parlour Aunty ta kawo ma NIHLA drinks da jallof rice Wanda yaji vegetables.

Gaishe ta NIHLA tayi, cikin farin ciki take amsawa, sannan suka gaisa da JAMAAL.

"Kun ishe mu da hayyaniya ka kwashe yaran ka ku fita"Aunty ce ta fad'i Haka.


Dariya yayi yace"kunji Yara na mu tafi abin mu"

Dariya su NIHLA sukayi gaskiya yaran sun burge ta.


Iman ce tace"A'a Uncle ni Zan tsaya gurin Aunty Mai kyau ce" ta nufa gurin NIHLA

Dariya sukayi gaba d'aya NIHLA tace"Zo Nan little d'ina ki zauna"


Hawa jikin ta Iman tayi tana murna, sosai JAMAAL yaji dad'in yanda ta nuna son yaran.




Haka sukayi hira sosai inda Aunty Jameela ta had'a magungunan Mata masu kyau na Sokoto, tasa NIHLA a gaba sai da ta shanye su, sannan ta Bata wasu tayi Mata bayanin yanda zata Sha, lokacin ne JAMAAL ya shigo yace zasu tafi, Nan sukayi sallama suka tafi.

 Lokacin da suka dawo RAUDAH ta gansu Nan taji wani azababben kishi.




Shiryawa tayi cikin wani nighties masu shegen kyau iya gwiwan ta purple colour Kuma net ne, ana ganin jikin ta ga breast d'in ta rabi duk a waje, sai ta d'aura after dress akai, ga k'amshi dake tashi a jikin ta, kwanciya tayi ta rufa da blanket.

JAMAAL ne ya shigo Yana sanye da short nicker da singlet, pillow ya d'auka da wani blanket yasa kan carpet, har ya kwanta ko meya faru kawai sai ya dawo kan bed ya kwanta kusa da ita.

Da sauri ta zauna "wani irin iskanci ne da zaka kwanta anan"

 Gyara kwanciya yayi yace"idan iskanci kike so sai ki fad'a min ba Wai ki dinga kwana-kwana ba, Kuma daga yau anan zan dinga kwana dama can ai nawa ne sai zuwan kine Zan koma kwanan carpet to I can tolerate it"

 "Baka Isa ba in had'a gado da Kai, d'an iska kawai yaro da Kai mai zaka iya min"


Zaro ido yayi yace"Haka Kika ce Koh? Ai ko yau sai na nuna Miki ni cikaken namiji ne, dan *NAMIJI BAYA K'ADAN*(Na Aysha Ali garkuwa)"

Nan ya fara kissing d'in ta, ta ko'ina Yana romancing d'in ta, ture shi ta fara Amma ta kasa, da k'yar yayi nasarar cire mata after dress, lokacin da yayi ido biyu da Kyakyawar surar ta gaba d'aya rikicewa yayi cafkar breast d'in ta yayi yafara tsotsa, NIHLA ko gaba d'aya ta fita hayyacin ta, gashi ta kasa ture shi, kawai sai ta fashe mai da kuka.

Cewa take"D'an iska wallahi ka k'yale ni, d'an yaro da Kai baza ka iya Dani ba"

Cikin wani irin hali yace"Zan ko Baki mamaki"

Kafin tayi magana ya had'e bakin su.


Sosai sukayi ta kokawa, Wanda sai da k'yar ya samu nasara, inda ya nuna Mata shi cikaken namiji ne🙈


A Daren Nan NIHLA tasha azaba tayi *DANA SANI*(coming soon) fad'a mai cewa shi ba namiji bane, ai ko yanzu ta tabattar shi d'in namijin gaske ne, duk kukan ta Bai saurare ta ba har sai da ya maida ta cikakiyar mace,yayi farin ciki sosai samun ta a cikakiyar Budurwa wacce ta kawo budurcin ta gidan mijin ta,Haka yayi tasa Mata Albarka ko kula shi batayi ba, da kanshi ya taya ta, ta tsaftace jikin ta sannan suka kwanta barci, gaskiya a wannan Daren yaji wani irin feeling Mai k'arfi akan NIHLA.






*Budurcin ki gidan mijin ki*

 *Budurcin ki gidan mijin ki, y'ar uwa ki rik'e wannan abin da hannu biyu-biyu domin kuwa ba Abu ne na Wasa ba, Mata ku kula da kanku kussan irin samareen da suke zuwa gurin ku, idan har kunsan ba da aure suke son ku ba to ku rabu dasu, ba k'aunar ku suke ba, ki rik'e budurcin ki har ki Kai shi gidan mijin ki*












*Janih one love*💘











*UMMU BASHEER CE*
[26/02 12:28 pm] Sis Ummu Bashir: 🌹 *BA MU DACE DA JUNA BA*🌹

                   🌹

     { *Short and interesting story* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#[email protected]
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE 45~50*



*Akwai* wata Rana da NIHLA take kwance kan katifa, zuciyar ta sai tashi yake ta rasa what's happening with her, Kawai sai ganin wani k'aton k'adangare ya fad'o daga window'n d'akin, gashi murtukeke, bak'ikirin gwanin ban tsoro, wani irin ihu Mai k'arfi tayi a gigice, lokaci d'aya cikin ta ya murd'a tsabar tsoro ganin Yana k'arasowa kusa da ita. RAUDAH da ta jefo k'adangaren tana gefe sai dariya take Dan dama burin ta, taba NIHLA tsoro.


A dai-dai lokacin ne JAMAAL ya shigo gidan da gudu ya shige d'akin, tana ganin shi ta rungume shi duk jikin ta rawa yakeyi ta tsorata sosai, tambayar ta yake mene ne da k'yar ta nuna mai k'aton k'adangaren, Direct d'auka yayi ya jefar a waje, RAUDAH dake lab'e haushi duk ya cika ta.


Dawowa yayi ya rungume ta Yana rarrashin ta, a ranar ko Zama a d'akin ta k'i, tana parlour'n Umma, a kwanakin tana son tuwon Umma, Amma ranar tana ci sai amai tayi, ga zazabi da ya rufe ta lokaci d'aya, JAMAAL duk a rud'e yake gashi tak'i yarda suje hospital, Umma ko ta lura NIHLA ciki take da shi, sai tace JAMAAL ya barta ta huta, Kuma ta sanar mai NIHLA ciki take dashi, ba K'aramin farin ciki sosai yayi ba, Yana ta ma Allah godiya, dama akwai shi da son yara, NIHLA ko kunya ne ya kamata, Umma na fita d'akin yayi saurin rungumar ta.


   "I'm very Happy, Zan Zama Baba"

 Dariya tayi tace"Toh Baba k'yale ni please"😂

  "Allah Ina mutuwar son baby'n Nan"

 "Ni ma Ina son ku duka"💋

 Suman zaune yayi Jin furucin ta, "Wow my wifey dagaske kikeyi kina k'aunar mu"😍

 "I mean what I said, I loved the baby"😘

 Rungume ta yayi very tight cikin farin ciki.


 Ni ummu basheer Ina ganin luv lokaci d'aya😂.




Cikin sati d'aya sosai yake kula da ita da ririta ta ya shagwab'a ta sosai fa, Dan komai take so sai ya samo Mata, sunje hospital an tabattar musu da ciki 2 months take d'auke dashi, sunyi farin ciki ba k'adan ba.


RAUDAH da taji NIHLA nada ciki kamar zata mutu take ji, Nan ta yanke shawaran had'uwa da JAMAAL ta fad'a mai sirrin zuciyar ta.



 "Ni gaskiya pounded yam nake son ci" NIHLA ta fad'a Haka cikin shagwab'a da k'ara kwanciya kan jikin JAMAAL.

 "Duk abin da baby na ke so shi Zaki ci,oya Bari in je gurin Aunty Jameela in samo miki"

 Kissing d'in forehead d'in ta yayi, ya Mata bye.

Fitowa yayi k'ofar gida kawai sai yaci karo da RAUDAH da zata shigo.

"Yauwa Yaya na dama Kai nazo nema"

 "Ok ya akayi,Ina sauri ne Aunty'n ki na jira na"

 Wani irin bak'in ciki taji,sai ta daure tace"dama ...Ina...son in ... fad'a ma.."

Katse ta yayi ta hanyar cewa"come-on ki fad'a min mene ne kin tsaya kina in Ina"


 Daurewa kawai tayi tace"Yaya na jima da birne wani sirri a cikin zuciya na, nayi k'okarin ganin cire abin a raina Amma hakan yak'i yuwuwa, Na jima da kamuwa da ciwon so, Yaya ko kasan wa nake so?"

"A'a, wane ne?"

 "Kai ne nake so"

 A firgice ya kalle ta, "kin San me kike cewa?"

"Eh Kai ne nake so, Yaya Ina k'aunar ka, wallahi Zan iya mutuwa idan baka aure ni ba, Na jima Ina jinyar son ka, ka taimake ni ka so ni"

Gaba d'aya ya rasa Mai zaice Dan baiyi tunanin abin da zata fad'a kenan ba, gaskiya shi ya d'auke ta ne a matsayin K'anwar shi ba zai iya auren ta ba, kuma idan yace Yana son ta yayi k'arya.

 "RAUDAH da farko dai Zan Baki hak'uri gaskiya na d'auke ki ne a matsayin K'anwa na, idan naje Zan aure ki to tabbas na Yaudare ki Dan ko k'adan bana k'aunar ki a zuciya na sai dai Ina Miki son y'ar uwa ta, kiyi hak'uri ki samu wani mijin kiyi aure, Kinga Ina son NIHLA Mata ta, bani da sha'awan k'ara aure, Mata d'aya ta ishe ni a rayuwa Dan Allah kiyi hak'uri Kuma zanyi Miki addu'a Allah ya Baki miji na gari"

Wani irin kuka ne ya taho Mata da k'yar ta iya dannewa, tace"ba komai Yaya, tunda har baka so na,to wallahi na hak'ura domin Ina son auren namijin da yake so na, nagode sosai" Nan ta shige gidan su, shi Kuma ya nufa gidan Aunty Jameela Yana mamakin RAUDAH, shi a gaskiya ma RAUDAH Bata cikin irin matan da yake so, Bata da shape Mai kyau gashi Bata son aiki, tana da k'azanta, gaskiya ba zai iya auren ta ba, bare yanzu NIHLA ita ce farin cikin shi.



 Har ta fara barci taji dawowan shi, A hankali ya k'arasa gurin ta "baby I'm sorry har kin Fara barci Koh?"

  "Uhm nidai please ka bani sakwaran Nan in ci har mafarkin shi nake"😋

  "Hoo baby har dreaming kike,oya zo inyi feeding d'in ki"

A kan cinyar shi ta zauna ya dinga Bata har ta k'oshi Tasha ruwa sannan ya rufe ta da blanket sukayi barci.





Saura sati d'aya JAMAAL ya tafi Canada, sosai yake mak'ale Mata Dan baya son rabuwa da ita, Kullum cikin kula da ita yake,yayin da take Jin wani irin mugun son shi a zuciyar ta, har mamaki take yanda take k'aunar shi.


  Tana kwance kan kujera dake parlour'n Umma taji wata murya Wanda har abada baza ta manta ba, Muryan Mom take ji.


Mom ce ta shigo gidan cikin yatsina fuska take k'are ma gidan kallo, Umma ganin Babbar mace yasa tayi tunanin ko Y'ar uwa'n NIHLA ne Dan sune masu kud'i, cewa tayi"Hajiya barka da zuwa ga guri ki zauna"

 Tsaki mom tayi "ke yanzu nayi Miki kama da wacce zata zauna anan?, Ina y'a ta take?"

A wannan lokacin ne NIHLA taji muryan Mom da gudu ta fito.

Umma tace"wace ce y'ar ki baiwar Allah?"

NIHLA na ganin Mom ta rungume ta cikin wani irin tsananin farin ciki, hawaye Mom tayi tana cewa"My daughter I can't believe you're leaving here"

Cikin hawaye tace"I really missed you Mom"

 Umma tace"NIHLA mahaifiyar ki ce?"

  "Eh Umma itace,Mom ga mahaifiyar JAMAAL"

 Umma tace"Ah maraba lale bissmillah shigo daga ciki"

 Tab'e baki mom tayi tace"ban zo Dan in zauna ba nazo d'aukar y'a ta ce"

Gaba d'ayan su a rikice suka kalle ta, lokacin Kuma yayi dai-dai da shigowan JAMAAL gidan yaji wannan kalmar daya firgita shi.

Umma tace"A'a Hajiya ba za'ayi Haka ba"

 A fusace Mom tace"Dole ne in d'auki y'a ta yau Dan wallahi baza tayi irin wannan rayuwar na talauci ba, y'a ta tafi k'arfin ku"

 Da sauri NIHLA ta rik'e hannun ta taja ta zuwa d'akin ta.


JAMAAL ne ya k'araso gurin Umma "Umma na ki taimake ni kar ki Bari a raba ni da Mata ta, wallahi Ina k'aunar ta"

Cikin kwantar Mai da hankali tace"karka damu ba abin da zai faru sai alkhairi"

 Daga inda suke suna jiyo maganar su Mom, inda NIHLA ke cewa"Mom ya akayi Kika san Nan?"

 "Daughter dole in bincike inda kike, tabbas mahaifin ki baiyi Mana adalci ba da har ya raba mu, ya hana in zo inda kike, da k'yar na samu Aunty Shuwerh ta bani address d'in inda kike,Dan kullum cikin yin mata waya nake Ina rok'on ta har taji tausayi na, Dan Haka dama nace Zan shirya plan, yanzu Zan tafi dake Misra Dan har nayi Mana visa, kije ki zauna gurin Ummie na, har sai nasa ya Baki takardan sakin ki"


Gaba d'aya ta tsorata da Jin furucin Mom, Haka ma su JAMAAL.

  "A'a Mom kiyi hak'uri bazan iya binki ba, Ina son yin ma Dad biyayya a karo na biyu"

 "What do you mean NIHLA,nazo ne fa Dan tafiya dake"

 "Kiyi hak'uri Ina son Zama, Ina son miji na"

 A rud'e tace"are you out of your sense NIHLA,do you know what you're saying?, Ko kin manta ke wace ce?,kece fa NIHLA TAHIR , kyakyawa Mai ji da kanta, kud'i da dukiya kina dashi, kina da company inda kike aiki, driver ke kaiki duk inda zaki, Shin duk kin manta ko ke wace ce a lokacin but look at you now, duk kin rame kinyi duhu, kalla kayan jikin ki, kalla fuskar ki, NIHLA what's wrong with you, kefa Kika ce Baki son auren, what happened?"


 Cikin hawaye tace"mom I knew all that, na tuna ko ni wace ce Earlier,but now everything has changed, Mom yanzu ba nice NIHLA da Kika sani ada ba, Ni yanzu Mai kud'i da talaka basu ne a gaba na ba, duk Allah ne yayi su, tabbas Ada nayi kuskure da nake nuna jiji da Kai da nuna Isa, Mom ni yanzu Ina k'aunar miji na bazan iya rabuwa da shi ba, kiyi hak'uri kawai ki tafi"

 "Anya ba suyi Miki asiri ba kuwa, Anya kece y'a ta NIHLA da na sani kuwa?I don't think so, NIHLA ki dawo cikin sense d'in ki, kisan me kikeyi"


"Mom Ina cikin hayyaci na nasan me nakeyi, Ina son miji na bazan iya rayuwa Babu shi ba, Kuma Ina d'auke da ciki"

A firgice tace"Ciki? Kina nufin ciki kike da shi NIHLA, da wannan yaron d'an talakawa?"


 Cikin kuka tace"Mom please I'm sorry but just go, bazan iya binki ba"

 A fusace tace"Yau nasan matsayina a gunki, daga yau Ina son ki d'auka na mutu, Baki da iyaye a duniya kiyi rayuwar ki keda talakawan da Kika zab'a" tana fad'in haka tayi waje.


 Da sauri NIHLA tabi bayan ta tana cewa"Mom please wait, karki ce Haka"


 Mom ko kallon su Umma batayi ba ta fita waje inda driver ke jiran ta, NIHLA ce ta bita da sauri Nan JAMAAL yabi Bayan ta Yana Kiran ta.


 Shiga mota tayi yayin da NIHLA ke knocking d'in glass d'in window tana Kiran sunan Mom, ita Koh kawar da Kai tayi yayin da driver ya ja motar a guje, da gudu JAMAAL yayi saurin rungumar NIHLA saura k'adan motar ta ja da ita.


Kuka ta fashe mai da shi, Shiga da ita cikin gida yayi Yana rarrashin ta.


Haka Kaka wacce dawowan ta d'aga unguwa kenan, da Umma sai Bata hak'uri suke, Kuma yanzu JAMAAL ya tabatta da NIHLA tana k'aunar shi.





Har dare tana kuka shi Kuma Yana aikin rarrashin ta har ta hak'ura.




Cikin sati d'ayan Nan suna wani irin soyayya ne Mai zafin gaske domin wani irin shak'uwa sukayi da junan su. A yau ne JAMAAL zai tafi, NIHLA sai kuka take, Har airport driver ya Kai JAMAAL inda su NIHLA,Umma,Kaka da Abba suka raka shi.


Jirgin su ya tashi zuwa k'asar Canada✈

Yayin da ya tafi cike da k'aunar matar shi NIHLA,Haka ita ma suka juya gida cike da k'aunar mijin ta da kewar shi.







******************************



 NIHLA cikin ta ya tsufa, haihuwa yau ko gobe, sosai Umma ke kula da ita, Haka Kaka ma, kullum cikin waya suke da JAMAAL, Yana Jin lafiyan baby'n shi. Ta b'angaren JAMAAL ma ya maida hankali sosai kan karatu ya gama ya dawo Dan ganin matar shi, y'an Mata dayawa na son shi amma basa samun ko kallon kirki, Dan Burin shi karatu. Yayi watsi dasu.




Ranar wata Friday ne NIHLA ta tashi da nak'uda tun abun Yana Mata k'adan-kad'an har yayi yawa, Umma ta Gane, ba tare da b'ata lokaci ba aka nufa hospital da ita, Dan dama JAMAAL Yana karatu Yana wani aikin ne acan Kuma Yana turo musu da kud'i, duk siyayan kayan baby ma shi yayi acan sai ya turo musu.


 Cikin awa d'aya Allah ya sauke ta lafiya inda ta haifa yaro namiji Mai kama da mahaifin shi JAMAAL sak, carbon copy kenan inji ni Ummu Basheer.


Anyi taron suna inda yaro yaci sunan mahaifin NIHLA,suna Kiran shi da HANIF, yaro ne Kyakyawa, Haka NIHLA tayi wankan jego Mai kyau domin sosai Umma ta tsaya Mata, ta Zama kamar mahaifiyar ta, Haka HUDA na yawon zuwa. RAUDAH ko ta gaji ta hak'ura ta fito da miji tayi aure.



NIHLA ta cigaba da zuwa makarantar islamiyya sosai ta dage har ta sauke Al-QUR'AN, gashi ta k'ara kyau sosai, Dan ko suna cin abinci Mai kyau sannan Kuma ga tsafta, Koda yaushe JAMAAL cikin turo musu kaya yake har iyayen nashi ma, yanzu suna rayuwa cike da ban sha'awa.











  """""""""'''''''""""""""""""""""'''''''''''"""""""""""""""""





*Bayan shekaru Uku*

   *After three years*


A yau ne ake ta Shirin dawowan JAMAAL daga Abroad, NIHLA ce na gani, Masha Allah nace, domin ba k'aramin kyau tayi ba gashi ta dawo yarinya k'arama baza ku tab'a Gane Tana da shekaru ba, wani Kyakyawan yaro ne d'an kimanin shekaru biyu yaje gurin Umma.


Dariya Umma tayi tace"Wato HANIF baka son wanka Koh"

 Cikin maganar shi da Bai iya ba yace"Ci b'oye ni, ka Mommy ci gani"

 NIHLA ce ta k'araso gurin "Let's go and bath,ai na gan ka"

 Mak'e kafad'a yayi yace"A'a ban sho"

 "Daddy'n ka zai dawo kazo ayi wanka kaji miji na Mai kawo cefane"cewar Umma cikin Wasa.


 Da k'yar dai NIHLA ta d'auke shi tayi mai wanka, ta shirya shi cikin riga blue Mai check da ratsin white,sai white jeans, ta gyara Mai gashin shi Wanda yake kwance kamar na larabawa.



Abinci kala-kala ta shirya ma mijin nata, ga natural drink na fruit da ta had'a, gashi dama a shirye take domin ta gyara kanta sosai gurin Aunty Jameela. Fatar ta yayi smooth ga wani irin sihirtacen k'amshi Mai dad'in gaske da takeyi. Ko'ina na gidan kamar Koda yaushe k'al-k'al yake.








KANO STATE AIRPORT


Sanu a hankali yake saukowa daga stairs na jirgin, Kyakyawan saurayi ne kamar bature Haka yake cikin suit black,ga sunglass da yasa, a hankali ya shak'i k'amshin k'asar shi Nigeria, JAMAAL kenan Wanda dawowan shi kenan daga k'asar waje, Yana cike da Burin had'uwa da Matar shi da yaron shi tare da Family'n shi.



Wani driver ne yazo ya d'auke shi tare da mutumin Nan da yayi Mai komai na tafiya, inda suka gaisa, sannan suka nufa unguwar su JAMAAL.
















*Janih one love*💘







*UMMU BASHEER CE*


*For comments only 07030865952*

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *