Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Friday, December 7, 2018

bani na kashe taba Complete love hausa novel

adsense here
→BA NI NA KASHE TABA← PART 1 na bigboy isah
me yasa kakashe ta me tama kane da zaka kashe
musu ita banyi zatan zaka iya kisan kaiba
zaharaddin sannan ta sake shi daga shake mai
wuya da tayi idanun shi sunyi nare nare ta koma
gefe tana kuka a hankali idan shi cike da kwalla ya
durkusa yace momy wllh BANI NA KASHE TABA
cikin kuka ya karashe maganar yace amma nasan
ba wanda zai saurare ni ya fashe da matsanan cin
kuka abun tausayi ji sukayi ana girgiza get din
gidan kamar za'a karya shi Daga ji kasan katti ne
majiya karfi a kofar gidan sai cewa suke wllh a fito
muna da dan mafia nan bazamu yarda ba ya yanka
masoyiyar sa bale yaran mu da kannan mu ay wllh
bazamu yarda ba sai mun kashe shi shima. da
maman deeny da kuma shi kanshi zaharadeen din
duk sun firgita da jin kalaman jama'ar nan na kofar
gida tunani suke ya za'ayi lalai idan ta basu deenyta
kashe shi zasuyi shima tunani yake bazai iya mika
kansa ba idan ya mutu mahaifiyar sa wane hali zata
shiga. suna ta faman saka wannan kwance wancan
su kuwa matasan nan tuni sun gaji kuma sunga
anki bude get hakan yasa aka nemo jarkar man
fetur a cewar su idan suka ji an fara toya gidan sa
fito su kuma sai su kama zaharadeen din su kashe
kamar yadda suke zargin yayi kisan kai. haka suka
fara watsa fetur a gidan su momy suna cikin tunani
sai sukaji ana jika su da ruwan fetur da dai suka
fahimci fetur ne sai duk suka tsorata jikin su ya
fara bari suka rasa abun yi momy cewa take cikin
kuka ay kaga abunda ka jawo mana yanzu gashi
zasu toya mu da rai kamar wasu yan wuta lol.
deeny yace wllh momy BANI NA NA KASHE TABA
momy tace towa ya kashe ta hawaye kawai naga
ya sake zubowa a fuskar shi karan jiniyar motar
police suka ji a waje ana ta koran mutane da ke
kokarin cin nawa gidan wuta dan har an samo
ashana ana kokarin kyastawa police da duka suka
kori mutane suka je kofar gidan cikin murya me
karfi suka ce zaharadeen ka fito ka mika kanka ga
hukuma dan tabatar da rashin laifin ka ko kuma
laifin jikin shi na rawa sai kuka yake yana wallh
BANI NA KASHE TABA2 momy ta kama hannun shi
tace hakuri zamuyi mu rungumi kaddara isha allah
bazaka cutu ba kayi hakuri ka mika kanka ina ga
hakan zaifi sauki. a gare mu ta karashe maganar ta
cikin kuka haka ya tashi yana tafe yana hawaye
yana juyowa kamar ya bude get din kuma kamar ya
bari a cikin zuciyar shi kuwa yace gwara in fita a
kashe ni ma hakan zaifi min sauki ya kalla sama
yace allah ka fitar dani daga zargin nan da ake min
yana bude get wani police yayi carat ya damke shi
gam sannan wani ta kama hannayan shi ya maida
su baya aka samai ankwa a hannayan shi aka tura
kyyarshi har cikin motar police din mutane ne suka
fara jifar shi suna sai mun kashe ka wllh bazamu
barka ba haka yasa police din cikin hanzari ya
warci motar tasu sai police station ana zuwa aka
nufi sel da shi aka rufe ganin an rufe deeny a sel
yasa na tsaya nan ku biyu ni dan jin labarin

→»ku dinga comment
→»yan mata da samari ayi invite
→»dan momy na gaisuwa
↓Yauwa haka nakeso
comment↓
bigboy



→BANI NA KASHE TA BA← PART 2 na bigboy isa
a gidan su halima kuwa ganin su nayi jigum jigum
kowa yayi ta gumi sai hawaye hajja hauwa hawaye
take tana fadin zaharadeen ashe ba san halima
kake ba ashe duk san da kake na kaje ka kashe ta
ne kayi kudi da ita ta karashe maganar da fashewa
da kuka kacuce mu deeny kaci amanar mu ka
kashe muna yar mu wace ita kadai muka haifa. kiyi
hakuri maman halima wllh wllh wllh sai an kwatar
muna hakin mu sai inda karfina ya kare wllh bazai
kashe muna diya a banza ba sai an kashe shi
shima hawaye ne suka gangaro fuskar shi. jikin
fushi ya tashi ya fita hajja hauwa kuwa kanta a
kasa kuka kawai take. momy kuwa tana ji an tafi da
deenyta cikin hanzari ta dakko hajib dinta ta saka ta
fito da sauri ta kulle gidan kunya duk ta cikata duk
majalisar data wuce ana nunata ana cewa ga
mahaifiyar yaran nan da kashe budurwar sa haka
tata wucewa ana nunata har takai gidan su kawun
deeny wanda shine kanin mahaifin deeny da yake
allah ya amshi ran mijin nata wanda shine mahaifin
zaharadeen tana shiga cikin gidan da sallamar ta
aka amsa ta shiga suka gaisa da amina matar
kawo kenan aka zubo mata koko da kosai dama
bata karya ba amma ko kallan shi batayi ba saboda
abunda ke damun ta su kam basu san komai ke
nan ba saboda labari bai kawo musu nan ba amina
matar kawu tace mamar deeny lafiya naga duk
fuskar ki cike da damuwa daidai nan ne kawu ya
fito daga ban daki kallo daya yama matar yayan
nashi yagane ba lafiya ba alamun tasha kuka ya
karaso wajan a lokacin da yake tambayar ta lafiya
kuwa tana kallan shi ta fashe da kuka a lokacin ne
duk sukayo kanta suna menene ya faru mamar
deeny lafiya kuwa. nan ta fara magana cikin kuka
tana deeny ne da maryam ta maimaita3 har sau
uku cikin kuka ta kasa fada.amina ce ta kamata
tana rarashin ta sannan tadan rage kukan kawu
yace me yasama zaharadeen din da maryam
kuma? nan ta fara shesheka tana musu bayani.tace
maryam tun jiya da ta fita islamiya jiya da yamma
to bata sake dawowa ba har yanzu deeny kuma a
yanzu maganar da nake muku yan sanda sun kama
shi sun tafi da shi wai ana zargin shi da kisan kai
nan ta fashe da kuka su kuma duk suka kama
inalilahhiwa ina ilaihir raji'u
inalilahhiwa ina ilaihir raji'u
inalilahhiwa ina ilaihir raji'u
suke fasa
*****************
acan kuma DPO ne yasa deeny a gaba yana
bazaka fada mana gaskiya ka hutar da kanka kuma
ka hutar damu ba yace yalabai wllh wllh BANI NA
KASHE TA BA dpo ya kara kallan shi yace watto sai
jikin ka yayi tsami zaka fada ko?…… tsoran kar a
hada dani ne yasa na tsaya a nan nima
mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group
bigboy
.


→BANI NA KASHE TABA← PART 3
na bigboy isah
a ranar koni da nake gefe na tausayawa
zaharadeen irin dukan da yasha suna dukan shi
suna bazaka fada mana gaskiya ba shidai abun da
yake cewa kawai wllh BANI NA KASHE TABA. BANI
NA KASHE TABA FA. haka akaci gaba da narkar shi
wai yaki fadan gaskiya har saida ya sume.
***************maman deeny kuwa gidan kawu ta
koma da zama kullum cikin kuka tana tunanin halin
da ta tsinci kanta a ciki yaran ta biyu su duka ba
daya har gwara shi deeny ma tunda ansan yana
hannun yan sanda amma ita kanwar tasa maryam
kenan ba'a san inda take ba kawu yayi yawo har ya
gaji ya dawo gida yana yin sallama suka amsa su
mashi da sauri maman deeny ta mike tana fadin
angan ta anga maryam dina kuwa? gani tayi ya
sunkuyar da kanshi kasa alamun ba labari kenan ai
kuwa ta dora hannun wanta akai ta saka uban kuka
matar kawu dake gefe ita ce ta taso ta rungume ta
tana cewa haba maman deeny hakuri zakiyi kuka
ba namu bane adda'u itace ma fita a wannan lamari
ita ma hawayan ne a fuskar ta. salama suka jiyo a
kofar gida da sauri kawu ya fita dan ganin wake
sallama police yagani cikin kayan aikin sa dan
sandar ya mikawa kawo hannun suka gaisa sannan
dan sandar yace kaine kanin mahaifin zaharadeen
ko kawu yace kwarai kuwa nine police din ya ciro
wata farar takar da ya mikawa kawo yace wannan
san maci ne daga kotu ku gaugauta samun lauya
domin gobe gobe zamu shiga kotu a bisa kes din
danku dan yaki amsa laifin sa a hannun mu kawu
ya karba hannun shi har bari yake yace na gode
sukayi ban kwana har ya juya zai shiga gida dan
sandar yace amma fa ku gaugau ta samun lauyan
ku saboda gobe ko baku da wani lauya bazai hana
zamanan ba a gobe haka kawu ya koma cikin gida
cike da damuwa yana ta tunanin shi ba kudi gare
shi ba ga basu dawa kadara da zasu sayar su
dauka lauya. abban aliyu me ya faru maman deeny
ce ta je4 mai wannan tambaya bai ce mata komai
ba kawai takardar dake hannun sa ya mika mata ta
karba tana bude wa ta fara karantawa sai hawaye
tana tunanin a ina zasu sama lauya Barrister
fadilah ta tuna sai sukaji tace alhmdulilah suka juya
suna kallan ta itama juyowa tayi sannan tace inada
kawata Barrister fadilah nasan tabbas zata taimaka
min idan na nufe ta da wannan alamarin sannan
kwarariyar lauya ce itama. gaba daya sukace
alhamdulilah saiki tashi ki shirya maman aliyu ta
rakaki inji kawu.
mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group
bigboy






on-line 14.04 21:00
→BANI NA KASHE TABA← PART 4
na bigboy isah
******************
alamarin maryam kuwa ranar asabar tayi wankan
ta tasaka kayan islamiya tayi ayr kwaliyar ta ta
dauko jakar qura'a nin ta ta fito tace mama zan tafi
makaranta maman deeny tace to maryam adawo
lafiya ayi karatu da kyau tace to momy zamu dage.
har ta fara tafiya tayi taku uku sai kuma ta juyo
tace momy wai har yanzu su yaya zaharadeen
shida halimar basu dawo ba ne momyn tace wllh
kuwa kinga har yanzu basu dawo ba. maryam tace
uhm nidai na tafi karna makara sai na dawo bye
bye tafita tana tafiya tana tilawa dan karta manta
karatun da sukayi jiya sai ji tayi mota ta faka ta
gefan ta da yake dan titin yau weekend ba jama'a
sosai duk ana gida ana hutu wasu kartai biyu suka
fito a motar cikin hanzari suka kamata suka rufe
mata baki sannan suka jefata cikin mota sukayi
gaba da ita sunata tafiya kamar bazasu tsaya ba ita
kuma kuka take har ta gaji tayi shiru sai kuma ta
fara ajiyar zuciya. wayar ogan yan daban ne tayi
kara ya daga ya risina yace oga an cika aiki ga
yarinyar da ka ce mu kamo ta yanzu ma muna tare
da ita. kome ogan yace mai oho jinayi yace ok sir
ya kashe wayar ya mayar aljihu sannan ya juya ya
kalli yarinyar da idanun ta duk sunyi jawur yace
kuba marar kunya ba zaku gane kun tabo wuta mun
kashe dayar sannan kema an bamu umarnin mu
kashe ki amma ba zamu tashi a tutar babu ba sai
mun danaki tukun nan zamu kashe ki. hannu ta
dora a kai ta fasa wani uban iho hade da kuka.
wuka yaciro yace sheet yi mana shiru, kallo daya
zakawa mutumin ka gane bashi da imani gashi baki
ga wasu jaja yan idanuwa fuskar nan tashi ba
annuri sai kace hata damusa maryam kuwa ta kara
kankame jikin ta tana kuka ciki ciki ana cikin tafiyar
ne naga sun faka motar kome ya faru oho sun fito
duk su ukun ba mai fara'a a cikin su dayan naga ya
zagaya baya sannan ya dawo yace oga akwai
matsala fa munyi faci a bayan nan ogan ya daka
masa tsawa maryam dake cikin mota har dan
fitsari ya kufto mata dan tsananin tsora lol. ogan
yace bazaka kunce tayar ka koma baya wancan
dan garin ka wo mana faci ba ka tsaya kana wani
yen yen yen wuce daga nan dallah. cikin hanzari
naga wanda ake kira kumurci yaje ya fara kunce
tayar ya sabe ta akafada ya koma baya wato garin
da suka wuce to gashi dare ya fara yi shi kuma
ogan ya dauki gallan yace wa wanda ake kira da
mugu yace kai zanje wancan gidan man wanda
muka wuce a baya zan je in karo mai dan ina
tunanin wannan bazai karasa damu kano ba
sannan yace ka kula da wannan yarinyar sosai
kuma kasa ido a kanta sosai yace angama oga shi
kuma ya juya ya fice ya bi bayan kumurci suna
tafiya shi kuma ya shiga gaban mota ya kuna
music yana yi yana girgiza kai yana rawa ita kuma
maryam tunanin tserewa take yi sai sake sake take
yi can sai naga tayi a jiyar zuciya ko me ta tuna
oho nima cewa nayi my queen me kika tuna………
Naku   bigboy > whatsapp no 08096831009







→BANI NA KASHE TABA← PART 5
na bigboy isah
jakar ta naga ta bude ta ciro wani lacasera mai
sanyi kuma sai naga ta dakko wasu kwayoyi cikin
hanzari ta zuba a cikin kwalbar lacasera din shi
kuma mugu yana can yana jin music din sa har ya
manta tsaron mutum yakeyi can sai naga maryam
din ta dan matso tace bawan allah dan allah zan
sama breadi ko rabi ne zan dan hada shi da
wannan ne ince sai ta dago lacasera haba baaban
yana ganin lemo gashi dama yunwa yake ji ya
kwace kwalbar tare da cewa yar iska waya ce miki
yara suna shan irin wannan miko shi yana amsa
yaji da dan sanyi sanyi kuwa ya kafa kai sai da ya
shanye shi kaf sannan ya yi wurgi da robar
lacasera din waje ya juya ya kalle maryam yace ina
sauran nan take idan shi suka fara lumshe wa
kamar wanda yasha ya bugu. ita kuma a zuciyar ta
karku so kuga farin ciki sai dadi take ji.sai a lokacin
na kula ashe maganin barci ta zuba mai mutumin
ku ya langabe kai ya fara sharar barci hada
minshari. maryam din tana ganin haka sai ta bude
motar da sauri ta fito ai kuwa tace kafa me naci
ban baki ba nan ta ari ta kare tayi cikin daji da gudu
su maryam anga mutuwa saida tayi gudu 5 mint
sannan ta sama wani gidan fulani gari ne karami
duk yan filo ne a garin ji sai daka ake yi can kuma
anyi wa wani daga cikin yaran fulanin biki an dakko
makadi sai cashewa akeyi. alamarin su ogan yan
daba kuwa tare suka taho shida kumurci sai wajan
magari ba suka dawo tun daga nesa suke jin music
na tashi a cikin motar su ogan yace kutt lalai
wannan yaran zai ci uban sa har ya sama damar
kunna waka a motar nan kamar motar uban shi
zaici uban shi bari mu karasa tun daga nesa
kumurci yace oga yarinyar nan fa kamar bata mota
a fusace ogan ya juyo yace zan mare ka dan
ubanka kasan abunda kake fadi kuwa. to ka muna
shiru ai kuwa suna karasa wa sukaga mota wayam
ba maryam sama ko kasa can gidan gaba kuma
mugune sai sharar barcin sa yake tuna ogan yaje
ya bude gidan gaban ya kwada ma mugu mari.
cikin barci ya tashi yana iho yana wllh na tuba
bazan kuma ba. yana ta yan surutan shi dai ogan
ya daka masa tsawa wanda ni kaina saida na
zabura saura kadan in yarda wayar in gudu lol.
amma saboda tsabar juriya irin tawa tsayawa
kawai zan yi anan *************
ku sani wannan abunda ya faru da maryam kanwar
deeny ka sancewar itama tunda ta fita islamiya
bata kara dawowa ba…………Naku   bigboy > whatsapp no 08096831009


mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group
bigboy
on-line 15.04 08:12
→BANI NA KASHE TABA← PART 6
na bigboy isah
tsawar da ogan ya mai ita ce ta dawo da shi
hayyacin sa ogan jikin murya mai kara yace ina
wannan yarinyar?. nan fa mugu ya fara kame kame
yana. dama uhmm uhmm ogan yace dama me
bazaka fada ba saina rabama kai biyu ogan ya fiddo
wukar shi yace wllh kayi wasa zan raba maka kai
biyu. jikin mugu na rawa yace oga inaga sayan
lacasera ta biku baku hadu a hanya ba ni dai na san
na kwace mata lacaseran ta ina shanye wa barci
ya kwashe ni ban farka ba sai ynz wllh oga. nida
nake gefe dariya na kama yi ma mugu. tsawar da
ogan ya sake yi ita tasa na kama baki na nayi
shiru. ogan yace kasan me kake fada kuwa kana
nufin ta tsere yanzu kasan ko asarar nawa ka jawo
mana kuwa ga asarar yarinyar sannan ga na 3m
naira ogan ya jingina kai jikin mota yana wani huci
kamar zaki. shi kuma kumurci da yake gefe ji
sukayi yace alhamdulilah su duka suka kalle shi
yace oga yadda zamuyi kawai muhau motar mu
muyi gida tunda dama mai gida yace a kashe ta to
kaga kawai sai mu koma muce angama aiki duk
mun kashe su tunda kaga wannan yarinyar dai
bazata iya tafiyar da zata sama gari a cikin wannan
daji ba nasan zatai ta yawo ne har yunwa ta kashe
ta kaga mun cika aiki kenan HAHAHAHAHAHA
dariyar mugun ta ogan yayi sannan kamar hadin
baki su duka suka dauka HAHAHAHAHAHAHAHAHA
sai dariyar suke *************
maryam kuwa zuwa tayi wajan masu kade kadan
nan ta zauna ta fara tunanin maganar ogan yan
daban nan da yace mata mun kashe dayar saura ke
ita a tunanin ta to wacece dayar? amsar data kasa
bawa kanta kenan ta dago kanta sai kalle kalan
yaran fulani take can ta hangi wani bakin maciji ya
doso wajan wasu yan mata su biyu dake zaune a
gindin wata bishiyar bedi da gudu ta nufi wajan su
tana kutashi maciji maciji suma da gudu naga sun
watsa suna iho aradu mashiji aradu mashiji kafin
kace me samarin fulanin nan sun rufe macijin da
duka dama kunsan basa rabuwa da sanda ga kuma
wuka. ita kuma yar fulanin zagayo wa tayi tana
neman maryam data taimaka musu can ta hango ta
a inda take zaune da ta kuma yin tagumi abunta a
hankali yar filo ta matsa wajan ta a tsorace tace
hannuka ko maryam ta dago kai tace yauwa
sannun ki sannan yar fulani tace amma naga
kamar kai bako ne anan ko ko zaka iya fada min
sunanka? ita kam maryam abun ya daure mata kai
an maidata namiji bata san haka suke maganar su
ba mace a maida ta namiji namiji kuma a maida shi
mace. can dai maryam ta dago kai ta kalli bafula
tana tace nifa macece ba namiji ba kuma sunana
maryam. sai bafulata nan ta kwashe da dariya tace
kayi hakuri haka maganan mu take. taci gaba da
cewa ni sunana aneesat amma mutanan rigga nan
suna cemin anne. maryam tace gud nice name
aneesat. ita kuma anne budar bakin ta sai cewa
tayi kice naman aneesat lol. maryam ta kwashe da
dariya tace cewa nayi nice name. ina nufin sunan
yayi dadi sannan annee tace ohho hk kike nufi
kenan. haka dai suka ci gaba da hira tamkar
kawaye. wanda suka saba da juna can dama. dan
itama anne har waje ta samu ta zauna sai labari
suke maryam na mata dariya yanayin hausar su ta
fulani. anne tace………
mu hadu a whatsapp→ 08140027062 Group
maman sabir
on-line 15.04 14:45
mungode
mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group
delete
bigboy
on-line 15.04 15:27
→BANI NA KASHE TABA← PART 7
na bigboy isah
anne tace wai shin gidan suwa kika zo ne awannan
riggar tamu?. maryam ta sunkuyar da kai sannan
sai hawaye suka kwararo mata. tace sato ni akayi.
nan ta kwashe labarin duka ta fadawa aneesa.
anne tayi mamaki dajin wannan labari. ta gyada kai
tace tabb aradu kinyi gudun mutuwa. ko kin san
daga nan zuwa bakin titi tafiyar wuni guda ce kuwa
gamu wanda muka saba ma kenan. maryam ta
bude baki tace wuni guda fa kika ce?. annee tace
kwarai kuwa. maryam tace allah ne kawai ya cece
ni daga sharin su. anne tace yanzu kinga dare yayi
tashi mu tafi gida sai mu kwana tare. maryam tayi
godiya ta tashi suka tafi.**************
acan kuwa gidan kawu, kawu ne yake cewa wai ni
shin da ake cewa deeny yayi kisan kai wa ya
kashe?. hawaye ne suka biyu ta kan fuskar maman
deeny sannan tace gawar halima aka gani a motar
shi sannan gawar halima aka samu a cikin nan ta
kara fashewa da kuka. maman aliyu ce ke rarashin
ta tace kiyi hakuri yanzu tashi mu tafi gidan br
fadila din dakyar aka samu tayi shiru ita dai abun
ya mata yawa ba maryam ba zaharadeen din ta
tasa mayafi suka fita suka tsaida nafen sai gidan
barrist fadila. sunyi sa'a tana gida kuwa da yake ba
wani aiki suna isa ta tare su hannun bibiyu tasa mai
aiki ta kawo musu abinci da ruwa da lemo haka
kuwa aka kawo musu abinci aka girke a gaban su
ga lemoka kala kala. su duk hankalin su ba'a akan
abince yake ba su brfadila suke su ta fito su mata
bayani kawai. can after 5mnt sai gata ta fito daga
daki fuskar ta cike da murmushi tace a su maman
deeny manya ba'a ko ganin ku yanzu yaushe rabo
mu hadu. maman deeny kuwa murmushi ta nema
ta rasa duk batada sukuni. tace ai kune manya
bakwa ko neman mu. kallo daya brfadila tawa
maman deeny ta fahimci ba lafiya ba. taga duk ta
wani canza. tace maman deeny lafiya kuwa. haba
sai hawaye kamar jira suke dama nan ta kwashe
labarin duka ta fada wa barrist fadila sannan tace
yanzu haka sunce gobe gobe za'a shiga kotu
saboda baban halima ya kai kara. brfadila wani a
jiyar zuciya ta saki sannan tace tabdi babbar
magana. tace yanzu bari in shirya inje mu gana da
deeny inji kan lamarin ankama deeny ai bamuga ta
zama ba. maman deeny ta dan share hawaye
sannan ta kalla brfadila tace yanzu saiki fada mana
abunda zamu kawo dan allah ki ceci yaran nan
nasan bazai iya kisan kai ba kuma shike daukar
dawai niyar mu yanzu in bashi ya zamu yi gashi
maryam din ma bamu san inda tayi ba. cikin sauri
fadila ta dago kai ta dafe kirji tace maryam ta bata.
maman aliyu ce ta bata amsa tace kwarai kuwa tun
jiya data fita islamiya bata dawo ba har yanzu.
maman deeny kuka take sosai. fadila ta kalle su
cike da tausayawa ta taso daga kujerar ta ta dawo
kusa da maman deeny ta rike hannun maman
deeny sannan tace. ki kwantar da hankalin ki
isha'alahu zamuyi nasara kuma kibar maganar kudi
deeny ai dana ne sannan ta kara dacewa in allah
yayarda deeny zai fito ki bar komai a hannun na
yanzu zanje na sama deeny. maman deeny da
maman aliyu godiya suke kamar me sun rasa kalan
godiyar da zasu mata ma. tace ba komai muje
driver ya kai ku idan ya dawo sannan na shirya sai
mu wuce da shi station wajan deeny…………
mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group
bigboy
on-line 15.04 15:28
→BANI NA KASHE TABA← PART 7
na bigboy isah
anne tace wai shin gidan suwa kika zo ne awannan
riggar tamu?. maryam ta sunkuyar da kai sannan
sai hawaye suka kwararo mata. tace sato ni akayi.
nan ta kwashe labarin duka ta fadawa aneesa.
anne tayi mamaki dajin wannan labari. ta gyada kai
tace tabb aradu kinyi gudun mutuwa. ko kin san
daga nan zuwa bakin titi tafiyar wuni guda ce kuwa
gamu wanda muka saba ma kenan. maryam ta
bude baki tace wuni guda fa kika ce?. annee tace
kwarai kuwa. maryam tace allah ne kawai ya cece
ni daga sharin su. anne tace yanzu kinga dare yayi
tashi mu tafi gida sai mu kwana tare. maryam tayi
godiya ta tashi suka tafi.**************
acan kuwa gidan kawu, kawu ne yake cewa wai ni
shin da ake cewa deeny yayi kisan kai wa ya
kashe?. hawaye ne suka biyu ta kan fuskar maman
deeny sannan tace halima aka gani a motar
shi sannan gawar halima budurwar aka samu a cikin motarsa nan ta
kara fashewa da kuka. maman aliyu ce ke rarashin
ta tace kiyi hakuri yanzu tashi mu tafi gidan br
fadila din dakyar aka samu tayi shiru ita dai abun
ya mata yawa ba maryam ba zaharadeen din ta
tasa mayafi suka fita suka tsaida nafen sai gidan
br fadila. sunyi sa'a tana gida kuwa da yake ba
wani aiki suna isa ta tare su hannun bibiyu tasa mai
aiki ta kawo musu abinci da ruwa da lemo haka
kuwa aka kawo musu abinci aka girke a gaban su
ga lemoka kala kala. su duk hankalin su ba'a akan
abince yake ba su brfadila suke su ta fito su mata
bayani kawai. can after 5mnt sai gata ta fito daga
daki fuskar ta cike da murmushi tace a su maman
deeny manya ba'a ko ganin ku yanzu yaushe rabo
mu hadu. maman deeny kuwa murmushi ta nema
ta rasa duk batada sukuni. tace ai kune manya
bakwa ko neman mu. kallo daya brfadila tawa
maman deeny ta fahimci ba lafiya ba. taga duk ta
wani canza. tace maman deeny lafiya kuwa. haba
sai hawaye kamar jira suke dama nan ta kwashe
labarin duka ta fada wa barrist fadila sannan tace
yanzu haka sunce gobe gobe za'a shiga kotu
saboda baban halima ya kai kara. brfadila wani a
jiyar zuciya ta saki sannan tace tabdi babbar
magana. tace yanzu bari in shirya inje mu gana da
deeny inji kan lamarin ankama deeny ai bamuga ta
zama ba. maman deeny ta dan share hawaye
sannan ta kalla brfadila tace yanzu saiki fada mana
abunda zamu kawo dan allah ki ceci yaran nan
nasan bazai iya kisan kai ba kuma shike daukar
dawai niyar mu yanzu in bashi ya zamu yi gashi
maryam din ma bamu san inda tayi ba. cikin sauri
fadila ta dago kai ta dafe kirji tace maryam ta bata.
maman aliyu ce ta bata amsa tace kwarai kuwa tun
jiya data fita islamiya bata dawo ba har yanzu.
maman deeny kuka take sosai. fadila ta kalle su
cike da tausayawa ta taso daga kujerar ta ta dawo
kusa da maman deeny ta rike hannun maman
deeny sannan tace. ki kwantar da hankalin ki
isha'alahu zamuyi nasara kuma kibar maganar kudi
deeny ai dana ne sannan ta kara dacewa in allah
yayarda deeny zai fito ki bar komai a hannun na
yanzu zanje na sama deeny. maman deeny da
maman aliyu godiya suke kamar me sun rasa kalan
godiyar da zasu mata ma. tace ba komai muje
driver ya kai ku idan ya dawo sannan na shirya sai
mu wuce da shi station wajan deeny…………
08096831009




→BANI NA KASHE TABA← PART8
na bigboy isah
salama tayi ya amsa kanshi a kasa yanata faman
zubarda hawaye duk wanda yaga deeny a wannan
halin dole ya tausaya masa sbd tsananin duka da
yasha. takare mai kallo sannan ta sama waje ta
zauna tace sannu deeny da kyar ya dago kai ya
kalle ta yace yauwa sannu sannan tace sunana br
fadila nice lauyan ka mai kare ka ina san sannan
wasu bayanai game da abunda ake zargin ka da shi
da fatan ka shirya?. shidai kawai ido ya zura mata
sannan ya daga kai alamun eh. nan sukayi yan
maganganun su tana tambayar sa yana bata amsa.
daga karshe tace zamuyi nasara isha allahu kafin
nan ina so in sanar da kai cewa karka yi magana
biyu a kotu dan hakan zai iya jawo mana matsala
yace toh sukayi sallama ta tashi ta fice.
***** alhj sunusi kuwa wani kwararan lauya ya
nema ana ce dashi barristr bashir ya biya shi kudi
har 500,000naira da yake shi ya kasan ce mai kudi
ne kudin sa kuwa sanadin wani yayan shi ya,same
su wani compny da yayan ya bar mishi sunan
yayan nashi alhaji bashir matar shi daya saratu. da
daya allah ya basu sunan yaran nasu yazeed yaran
nasu yana jida kudin uban sa shi kuma uban ya
sakar mai duk dukiyar sa a cewar shi shi zai gaje
shi ay hajj saratu taita fada idan taga yanda alhj ke
sakar wa dan nashi kudi.
*******
wata babbar kotu nagani a cike makil da yan kallo
da wanda aka bukaci ganin su. kotu tayi shiru.
alkali kawai ake jira ba'a jima ba saiga shi ya shigo
ai kuwa duk jama'a gaba daya aka mike alkali ya
nufi set din sa ya zauna .an fito da zaharadeen
cikin ankwa duk wanda ya kalle sa saiya tausaya
mai alkali yace assalamu alaikum warahmatul lahi
wabarakatuho.
duk jama'a suka amsa sannan alkali yaci "court
clerk call the
case" Court yafara bayaninsa "In the case of
murder between zaharadeen kabir and alhj sunusi.
yaci gaba da bayanin sa muna bukatar lauyoyi su
gabatar muna da kansu. ya koma ya zauna. my
name is barrister bashir lauyan mai kara shima ya
koma ya,zauna.fadilat ta mike my name is barrister
fadila mai kare wanda ake tuguma. sai duk kotu
tayi tsit har yan wajan ma kowa yayi shiru. babu
wanda bai hallara a wajan ba.maman deeny.amina
maman aliyu.alhj sunusi da matar sa. da wanda
yaga gawar da duk sauran jama'a dai duk sun
halara har da baban yazeed da maman sa duk…………08096831009








→BANI NA KASHE TABA←PART 9
na bigboy isah
br bashir ya nema alfarma ga kotu domin ya fara
tambayoyin sa. kotu tamai izini. sannan yaje gaban
deeny. yace zanso sanin cikeken sunan ka. ya
dago kai yace. sunana zaharadeen kabir. br bashir
yace. miye hadinka da halima. deeny yace budurwa
tace. duk jama'a suka dago kai suka kurawa deeny
ido.kai ka kashe halima?.deeny yace BANI NA
KASHE TABA. br yace an tabbatar da anga gawar
halima a motar ka muna da sheda ba daya ba ma.
yace haka ne. br yayi ajiyar zuciya. sannan yace to
waya kashe ta?. deeny yace nima ban sani
ba.bashir yace zaka iya fada mana dalilin ka na
cewa bakai ka kashe taba kuma bayan antabatar
kai kazo har gida ka dauke ta?. deeny ya fara bada
labari. ranar washe garin ranar da dare mu kayi
waya da halima take cemin dan allah gobe inzo mu
tafi yawan shakatawa ita kafin hutun su ya kare
tana so ta dan ga gari. da har naki amincewa nace
ni ba inda zani yawan shakatawa ay na masu
kudine muda muke nema ina mukaga samun damar
zuwa wani shakatawa. ai kuwa nan ta fashe da
kukan shagwaba wai ita wllh sai yazo ya dauke
ta.dai dai nan hjj hauwa ta shigo dakin halima ta
isketa da dan kukan ta hada hawaye. da sauri ta
karasa tace halima lafiya kuwa.tace momy lafiya
lau ba komai. hjj hauwa tace ban yarda ba sai kin
fada min. alokaci shi deeny kuwa yana saurarn su.
sai halima tayi sauri ta katse call din ta kamo wani
video fassara tace momy fin ne nake kallo shine
abun ya bani tausayi nake hawaye. momy dariya
tayi tare da cewa allah ya shirye ki. sannan ta
kama hanya ta fita. tana fita daga dakin. halima ta
sake kiran deeny duka daya ya daga wayar kamar
dama jira yake. yana dagawa yace kin gama
kukan. tace pls dan allah kayi hakuri kazo mu fita
gobe. yace kwantar da hankalin ki gimbiyata zanzo
isha'alahu ai kuwa dan murna hada tsale sannan
tace gobe karfe 10 ka shirya ko anguwar mu
sannan baban na ya fita nasan yada zanwa momy
ta barni in fita kaji yace to.allah ya kaimu haka taita
jin dadi. har allah allah take gari ya waye. ai kuwa
gari na waye wa ta yi sallah ta fito farllo sukayi
breek sannan momy ta dakowa dady jakar sa zai
fita dan har ya makara yanzu karfe 9:30 suka raka
shi har mota halima ce rike da jakar sai da ya shiga
mota sannan ta durkusa ta mika mai ya amsa yace
baby allah ya miki albarka tace amin sannan ya
juya yawa maman baby bye bye driver yaja shi
suka fice yana su kuma suka koma farllo suna
kallo ita kuma halima duk tabi ta damu ta rasa
wace karya zatayi ga waya a hannun ta sai
jujuyawa take. hjj hauwa ta fahimce ta tace ke me
yake damunki ne naga duk kin changer fuska.
halima tace momy mun dan sama sabani ne da
deeny wai shine yace inje yana kofa zai
bani.hakuri. momy tayi murmushi tace kude yaran
nan bakwa gajiya da rikici ko shiyasa naga jiya kina
hawaye. ta sadda kanta kasa. momy tace hmm
shiyasa naga bai shigo ba kenan yasan yau ba a
shirye kuke ba ay saiki tashi ki fita. halima
a,zuciyar ta cike da farin ciki a fuska ko kamar
bata so. ta tashi ta shiga dakin ta tayi yar kulleyar
ta sannan ta chanza kaya. wata atamfa ta saka mai
kyau green & water riga da siket sun mata cip cip
sun kara fito da kyan ta ta dau gyalan ta fari ta yafa
sannan taje jikin mirror ta kalla kanta tayi
murmushi sannan ta fice a dakin …………
mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group
bigboy
on-line 17.04 12:52






→BANI NA KASHE TA BA← PART 10
na bigboy isah
ta fito tace momy na tafi momy tace to a dawo
lafiya kuma kice ina gaida shi tunda shi yau bazai
shigo ya gaida mu ba. tace ameen momy zai ji.
ta fita da murnan ta ta nufi inda yake a mota ta bude
motar ta shiga sannan tayi ajiyar zuciya tace to sai
motafi ko ina zamu fara zuwa. wani kalan kallo ya
mata mai cike da so da kauna. yace saida kika
wahalar dani na zo sai jira nake kinki fitowa. ta
mararai raice tace haba sweethr kasan irin faman
da nasha kafin in samu a barni na fito kuwa sai da
nayi karya fa. gaba daya suka kwashe da dariya.
sannan yaja motar yayi gaba suna tafiya suna ta
zuba hirar su ta soyayya tana tamai shagwaba kala
kala tace wannan yatsaya ya saya tace wancan
haka dai suke ta tafiya suna soyayyar su abun
gwanin ban sha'awa. sune har wajan la'asar yace
tabari tunda ga masalaci a kusa kuma ankira sallah
to tabari yayi sallah tunda kinga ko sallahr azahar
banyi ba. tace to nifa nima ay banyi ba. yace ai ku
mata ne kun saba dama idan ana biki sallar huni
guda duk kuke hadawa lol. ta jefo mai bisket din
hannun sa ya kare da hannun sa kuma ya fita da
gudu yana dariya itama dariyar take. ita kadai a
mota shi kuma ya nufi masalaci ya dauki buta ya
zuba ruwa ya nufi ban daki.
kotu dai tayi tsit deeny kadai ake ji sai zuba labari
yake nima ina gefe ina sauraran sa.
yace bayan na gama sallah ne na nufi mota ina
zuwa na iske halima a kwance ni a tunani na barci
take haka nayi murmushi nace yarinya ai gobe
bazaki kara cewa a taho yawan shakatawa ba
gakinan duk kin gaji har kinyi barcin dole. ni kuwa
nace deeny ka kashe yarinya kace barci take ko
lol. yaci gaba da jan motar shi bai tsaya ko inaba
sai gidan su halima yana zuwa ya tsaya a kofa
yakama dan babuga ta yana cewa my luv tashi
mun iso my heart ki tashi ko duk gajiyar ce haka.
yayi yayi yaga ko motsi taki yi. nan fa duk ya rikice
ya shiga gida ya kira mai gadi wai yazo ya tada mai
ita ta shiga gida. ni duk a sannan ban fahimci
halima mutuwa tayi ba inji deeny. mai gadi yazo
yace ban gane in taya ka tadata ba mai ya faru.
deeny yace nidai nayi nayi taki tashi kuma daga yin
barci. mai gadi ya matsa kusa da ita ya kama
hannun ta ya daga ya sake shi yaji hannun ya dawo
kamar dai yadda gawa take. shima duk bai gamsu
ba tukun ya bude idan halima yaga fari fat ai kuwa
dama tsoho ne da gudu ya ban kade deeny ya nufi
cikin gida.deeny har zai bishi sai yaji mai gadi na
cewa hajiya ya kashe miki yarinya…………
mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group
bigboy
on-line 18.04 18:45
→BANI NA KASHE TABA← PART 11
na bigboy isah
deeny da gudu yayi baya duk jikin sa na rawa ya
fizgi mota yayi ciki gudu yake ba kaf kaftawa yace
ban tsaya ba nabi wani barji a tunani na duk wajan
daji ne ba mutane. yace haka na je na tsaya da
mota na juya ina ta kallan halima ina kuka a zuciya
ina cewa wai yanzu halima ta ta mutu kenan. nan
hawaye suka fara zarya a fuskata na fito na dauki
halima. wai ni a nufina binne ta zanyi idan na koma
gida koma me za'ayi sai ayi. ina tafiya inata sake
sake na dan yi nisa da mota ta nan na ajiye halima
inata kuka ina jijigata ina cewa ki tashi ki tashi.
shiru nine har magariba ina wajan nan fa na gaji sai
kawai na fara haka rami da yake wajan ba tauri nayi
rami mai dan tsawo nan kuma sai na tsaya ina
tunani toh in binne ta anan ko kuma in maida ta gida
a mata sallah a sa mata lukafani. inata saka
wancan kunce wancan. sai ji nayi ance waye nan
ban ankara ba sai ganin kibiya nayi a gaba na ta
caki kasa ina juyawa naga wani saurayi ne ya
durfafo ni hannun shi rike da kwari da gwafa. ashe
wai nan garkar rogwan sune wai yana ce ni
barawan rogo ne lol. da gudu na bar waje nayi
wajan motata sai na danyi gudu kadan sai na tsaya
a zuciyata nace gwara in tsaya in cemai yar uwata
ce ta mutu shine zan binne ta. wata zuciyar kuma
tace wannan da yake fada a kan rogo baya ko
tsayawa a mai bayani toh ina zai tsaya sauraro
na.yana cikin hakan sai ganin mutum yayi a guje ya
nufo shi yana barwo aradu barawo ne. ni kuma sai
nake cewa ka tsaya ka saurare ni. haba ba sai ji
nayi ya sako wata ki biyar ba badan na guce ba da
sai ta same ni. da gudu na fada mota naja ta da
gudu ya biyo ni. yana har bi yana jifa har dai na
samu na tsere. can naje bakin titi na ajiye motar
sannan na taho a kasa sai dai ina fargaba amma a
haka nace kai gwara inje duk abunda zai same ni
ya same ni amma sai na dako halimata na nufi
garkar na dan bi a hankali na leka nayi zatan yana
nan. amma sai naga wayam tun a nesa naji gabani
yana faduwa da na hangi wajan da na ajiye halimata
ba komai a hajan tun a nesa na dora hannuwa a kai
ina isa wajan kuma na iske ba komai a wajan sai
dai ga dan ramin da nayi nan. haka nata ratsa daji
ina neman saurayin nan ko sama ko kasa na
nemeshi na rasa. bana jin kukan komai a wajan sai
kukan tsintsaye da na dabobi da yake dare ne
rananr dai haka nata yawo ina kuka kamar
mahaukaci ina tunanin shikenan na rabu da
masoyiyata abar kaunata hasken zuciyata bugwan
zuciyata. na fashe da kuka a ranar duk wani tsoro
ya fita a raina bana jin ko tsoran duhun dajin nan
haka na hakura na koma naja mota na inata tunane
tunane. na nufi gida…………
mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group
.




bigboy
on-line 19.04 09:54
→BANI NA KASHE TABA←PART 12
na bigboy isah
TUN DAGA BAKIN KOFA naji gabana yana faduwa
duk tsoran maman mu nake. sai kuma nayi tunanin
ay bata san komai ba. kawai na shiga gida na nufi
daki na na kwanta. banyi barci ba har safe da
asuba nayi sallah a daki dumin bazan iya fita ba duk
na gaji saboda yawan da nasha jiya a daji ina gama
sallah na nufi dakin momy ai kuwa ina isa kamar
ance mata gani nan sai saukar mari naji tass tace
ina kakai musu yarinya nasan bazaka iya kisa ba
amma ina kakai.musu yarinya.nace mama wllh
BANI NA KASHE TABA momy ta zaroo ido dagaske
ta mutu. ai kuwa ta shake min wuya tana cewa. me
yasa kakashe ta me tama kane da zaka kashe
musu ita banyi zatan zaka iya kisan kaiba
zaharaddin sannan ta sake ni daga shake min
wuya da tayi idanuna duk sun cika da kwala. momy
ta koma gefe tana kuka. a hankali na durkusa nace
momy wllh BANI NA KASHE TABA ana nan yan
anguwa suka zo zasu toya mu sannan police suka
kore su aka kamoni akayo nan dani. ya mai girma
mai shari'a wllh gaskiyar abun da na sani
kenan.mustapah ne yace yallabai wannan ba abun
kamawa bane idan kayi la'akari da maganganun sa
akwai karya a ciki sannan yace na gode ya mai
shari'a. sannan alkali bayan yagama yan rubuce
rubucen shi yayi aziyar zuciya sannan yace
barrister fadila fa tana da tambaya. tamike tace
akwai ya mai shara'a. tace ina rokon kotu data bani
izini in kira hjjy karima maman deeny.alkali yace an
baki izini. ana bukatar ganin hjj karima maman
deeny. ta taso taje ta tsaya a inda aka tana.br
fadila tace da farko muna bukatar jin sunan ki dana
mijin ki.ta goge dan hawayan dake fuskar ta domin
ta tausayawa yaran nata. tace sunana karima mata
ga alh kabir . fadila tace wannan fa danki ne
kokuwa dan riko ne. maman deeny tace dana na
cikina. fadila tace maganar da ya fadi duk gaskiya
ne haka sun faru. maman deeny tace duk abun da
ya fada dangane da ni haka ne. tun safe ko karin
kirki baiyi ba yace min zashi gidan su halima da
yake ni nasan tsakanin su shiyasa ban tugume shi
mai zaiyi a can din ba. haka naita jiran shi amma
shiru bai dawo ba kanwar shi ma kuma haka da ta
dawo daga school ta takura min da tambaya ina
yaya deeny sai dai nace ya tafi gidan su halima. da
yake itama halimar kawar ta ce.har tayi shiri
makarantar islamiya amma deeny bai dawo ba
abun ya daure mana kai gaba daya. yaran da yake
cin abincin rana a sai gashi har 3:30 bai dawo ba.to
bayan fitar maryam ne ba'a jima ba sai ga mai
gadin gidan su halima da yan sanda wai sun zo
kama deeny anan ne suke shaida min wai ya kashe
halima. na dafe kirji sakamakon hani mumanan
faduwar gaba da naji. sannan na fada musu rabona
da shi. amma basu hakura ba suna ce boye shi
nayi duk saida suka har gitsa gida suka shiga ko
ina amma basu samai ba. suna gidan tun lokacin
har bayan isha'i amma bai dawo ba. ni kuwa abun
duniya ya isheni dan a lokacin har jini na ya hau.
saboda yada abun suka min biyu ga deeny ana
zargin shi da kisan kai sannan ga maryam bata
dawo ba. hakan yasa na shiga daki na kwanta
zazabi ya rufe ni ban tashi ba sai da safe………………08096831009












→BANI NA KASHE TABA← PART 13
na bigboy isah
barrister fadila. tace mun gode. zaki iya komawa
mazaunin ki. sannan br fadila tasa akata kira
mutane daya bayan daya. daga kan maman halima
har mai gadi duk wanda labarin deeny ya shafa. sai
yace eh maganar da ya fada gaskiya ce. barrister
fadila. tace ina rokon wannan kotun mai adalci data
rike labarin wannan bawan allah karta dauke su a
karya. bayan ga shaidu mun samu kuma duk sun
tabbatar da zancen sa haka ne. sannan ina rokon
kotu da ta tura jami'a tsaro dumin su tafi da deeny
ya kaisu har wannan wajan da yayi rami dan
tabbatar da gaskyar sa. na gode ya mai shari'a.
deeny kuwa duk ya tsure dumin a lokacin bai san
ma inda ya tunkara ba balle ya kai wanda za'a hada
shi da su yanzu. turkash. alkali yace munji kuma
mun yarda da zan can ki barrister fadila gobe za'a
hada shi da jami'an tsaro dumin su je su bincika
dan tabatar da gaskiyar sa sannan mun dage
wannan zama har zuwa jibi. alkali ya buga
gudumarsa…………kotu ta watse >>>>> cigaban labrin deeny>
lokacin da dan fulani ya dawo wajan sai ya tarar da
mutum a kwance kuma ga duk kan alamu wancan
da ya kora binne wannan din yazo yi. adan tsorace
ya nufi wajan a hankali ya juyo ta sai yaga ashe
macece ma daya kula sosai sai yaga da sauran rai
da sauri ya sabe ta ya nufi gida da zuwa kuwa
gwaggo ta tarye shi suka kamata suka ajiye a kan
wani gadan kara ita kuwa har yanzu bata dawo
hayyacin ta ba. nan gwaggo take tambayar isah ina
ka samu wannan yarinyar gata kamar yar bunni.
tana dan jujuyata.isah yakwashe duk labarin
abunda ya faru ya fadawa gwaggo gwaggo tace to
hike nan allah hukumusa'a. ya tashi yace gwaggo a
kula da shi ni na komai dawa. da yabi kwari da
gwafan shi yayi ciki.
da sasafe halima a hankali ta bude ido ta ganta
cikin bukka tayi mamaki sosai. a hankali ta taso
jikin ta ba kwari. tana tagal tagal. gwaggo ta taho da
gudu ta tare ta daga faduwar da zatayi. ita kuma
halima deeny take ta kira tana ina deeny na. deeny
nan inane. duk ta wani rikice. gwaggo tace kiyi
hakuri mana ki saurare ni nan ba garin ku bane.
nan kina cikin rugga ne. halima ta zaro ido rugga
kuma. gwaggo tace tabbas kuwa. jika na ne ya
tsunto ki jiya a can garkar su wani na kokarin binne
ki. halima tayi ajiyar zuciya tace yanzu ko wane
hali mamana da abbana suke cikin. hawaye kawai
suka shararo mata. gwaggo tace jikin ki ba kware
muje ki zauna. ai kuwa haka gwaggo ta taimaka
mata a hankali taje ta zauna…………>
mu hadu a https://m.facebook.com/groups/1232550283531628.


 whatsapp→ 08096831009 Group
bigboy
on-line 21.04 11:05
→BANI NA KASHE TABA← PART 14
N@ BIGBOY isah
acan kuwa bangaran maryam tashe sukayi suka
nufi gidan su anne. suna shiga suka iske iyayan
anne a tsakar gida suna hutawa suna yar hirar su.
suka karasa maryam ta gaishe su suka amsa cikin
fara'ar su sannan maman anne tace aneesat
wannan fa daga ina haka kamar yar bunni. anne
tace yar bunni ce mana yan fashi ne suka sato
ta,zasu kashe ta shine ta tsero har allah ya kawo ta
nan kuma a dandali muka hadu tataima ka mana ta
nuna mana maciji zai sare mu. shine har nake
tambayar ta gidan suea tazo sai ta bani lbr shine
nace bari muzo nan gidan ta kwana kafin akaita
garin su.abban anne yayi murmushi yace allah ya
miki albarka kinga dadin zaman birni kenan yaci
gaba da cewa ni naso in sama kudi ma a wannan
shekarar mu koma birnin nan mu duka har gwaggo
da yayan ki ya kalle anne. maman anne tace wllh
malam ba inda zaka halan kaje ka likewa wata kace
auranta zakayi ko wllh baza mu ba toh. su anne
gaba daya suka kwashe da dariya har maryam
dariyar take. ai kuwa sai gani nayi. maman anne ta
tashi ta shiga bukar su. nan anne da maryam da
baban maryam sukaita hirar su. maryam kuwa ta
saki jiki.baban anne yace aneesat tashi ku tafi daki
kusha fura sai ku kwana daki daya keda bakuwar
taki ko. anne tace to abba. suka shiga dakin daga
wani gadan kara bazai ci mutum uku ba na mutum
biyu ne ko katifa babu sai tabarmar da aka shin fida
da kuma barguna. da yake anne mai tsafta ce dakin
yar bukkar tata tsaf tsaf da ita. gefe kuma ga yar a
kwatin ta. hada nunawa maryam wai yayan tane ya
sayo mata. kuma duk ruggar nan babu mai kalan
ta. maryam kuwa me zatayi banda dariya. taga an
dakko wata tsohuwar akwati wai nan abu mai
daraja ne a garin. nan dai suka gama shirman su
suka gaji da hira suka kwanta. ai kuwa ranar da
dare maryam tasha jifga.daga anjima sai dai taji an
laf to mata kafa ta janye ana jimawa ta kara jin an
wullo mata. maryam tace na shiga uku wannan
kamar mage dai wannan ai mijin ki ya shiga uku. a
haka dai har asuba tayi. maryam ta tashi ta fito ta
dauki buta dama annee ta nuna mata bandaki. ta
fito tayi alwala. sannan taje tayi sallah tayi
adda'au. nan fa ta fara tunanin maman ta da kuma
yaya deenyta. tana cikin wannan tunanin taji matsin
anne ta farka ta murge ido taga maryam a kan
sallaya. tana kallan ta. tace ke kuma haka ake a
garin ku kita shi kiki tada mutane ko. maryam tace
ke tada ki ai sai jirgi ko kuma azo da bulala. anne
tace to miyasa baki dakko bulalar ba. maryam tace
ba komai ai akwai gobe. da sauri anne tace toh
gobe me zakiyi?. tace ahah bulala zan samo mana
saboda tada ki ba kince mi isa ban samo bulala ba.
anne tace wasa nake miki kinji yar kawata. ai
wannan lalausan jikin nawa bazai dauki bulala ba.
gaba daya suka kwashe da dariya. maryam tace.
katashi ka nema ruwa ka yi alwala kazo kayi
sallah. anne tace kai abun hada tsokala ai dai
allahn da yasa ni maganar fulanin ma bata kama
baki na ba.kinsan mu a burni muka girma. maryam
tace wai ina wannan yayan naki yake ne. sai kira
kike yayan ki yayan ki. anne tace yayana yana
gidan gwaggo gwaggo ta kwace mana shi ay. tace
bari dai in tashi wannan hirar ba karewa zata yi ba.
ta tashi taje tayi alwala. ta dawo ta iske maryam
tayi tagumi sai tunani take. anne tace maryam
maryam.firgigit ta dawo hayaccin ta daga tunanin
da take. anne tace kinga indai gida ne ki kwantar da
hankalin ki. yanzu da muka gaisa da mamana tace
gobe zata bawa yaya isah kudin mashin ya maida
ki garin ku. cikin fara'a da murna tace wow na gode
na gode. sosai.sis.anne tace bari inyi sallah ki
rakani zan kaiwa su gwaggo abin kari. maryam
tace toh shikenan………<
mu hadu a  https://m.facebook.com/groups/1232550283531628     whatsapp→ 08096831009 Group
bigboy
on-line 21.04 11:08
→BANI NA KASHE TABA← PART 15
N@ BIGBOY isah
>tunda sasafe police uku tare da deeny suka hau
mota suka nufi daji shidai deeny ba zai gane
wannan garkar ba wacce yaje yayi rami haka sukai
ta shara gudu deeny na nuna hanya duk da ba gane
wajan yayi ba saboda da dadare ne shi sadda yazo
ana tafiya da ya hangi wasu garake can nesa yace
toh a tsaya aka tsaya aka firfito daga motar.
yansanda suka sa deeny a tsakiya har suka kunce
mai unkwar dake hannun sa wai a cewar su ya
za'a yi wannan dan yaran ya iya tserewa daga
hannun mu mu uku. ni kuwa dake gefe ido kawai
na zuba inga mai zai faru. haka sukai ta tafiya suje
wannan garkar suga babu rami deeny kuwa ya fara
tsurewa dan ya sare ganin ba'a gane karkar ba. a
haka suje wannan yace inaga wacan ce su kara
gaba yace la na tuna wacan ce wllh. sai da ya
musu haka wajan sau 15 sannan suka ce kai zamu
ci uban ka fa ya zaka raina muna wayyo kaita sako
mu cikin daji. sai daya ya juya baya yaga baya
hango titi balle motar su. yace kan uba. ku duba
baya. suka waiga suma sunyi mama kin nisan
da,sukayo. daya ya falle deeny da mari yace dan
uban ka dama karya kake. deeny yana sheshekar
kuka yace wllh yallabai ba karya nake ba. can
deeny ya daga kai yaga wata garka can makekiya.
yace yallabai wllh kaga garkar can.suka ce lalai ka
raina mana wayoo wajan sau ashirin fa kenan kana
muna haka. amma karka ce mun kware ka da
sharadi. kaga daga nan zuwa garkar can da ka
nuna yanzu da nisa ko. deeny yace haka ne. police
din wanda shine babba a cikin yan sandan yace. to
idan muka je mukaga ba haka bane. wllh ka kuka
da kanka dan wllh sai mun zanee ka kuma kayi
tsallan kwadi tundaga wajan har nan. deeny gaban
shi na faduwa yace naji. na yarda. suka kama
hanya suka nufi garkar deeny kuwa gaban shi sai
faduwa yake yaji irin abunda za'a mishi idan ba
garkar bace. ai kuwa tun daga nesa ya hangi wani
rami irin an cire rogo a wajan ai kuwa ya fara
murna. sukuwa hararan shi kawai suke. suka
karasa bakin ramin. daya ya kalli deeny yace dan
ubanka wannan rogo aka cira a wajan ba ramin da
kace kayi bane. deeny duk da yasan ba shi bane
amma haka ya rike gardama wai wllh shine. deeny
hada hawaye yana tunanin idan aka koma kotu fa
hukuncin kisa za'a yanke mai bayan wahalar da
zasu bashi a nan.
yana cikin tunani. su kuwa har sun aika a ciro
bulala. haba sai ganin wanda aka aika nayi ya dawo
a guje yana fadin kura kura. su kuwa cewa suke
dalla can a wannan dan dajin ya za'a yi a sama
kura. deeny kuwa add'au yake allah yasa kurar ce
ma ya samu ya tsere. suna juyawa kuwa sukaga
wani katan kare kai saika ce kura. karan baki wul
da shi ga gashi kamar buzun kare. suka ce wa
wanda ya rugo yana cewa kura.,banza ashema
kare ne kake cewa kura. bari mu kashe. wannan
dan iskan karan. ai kuwa suka nufi karan da
kulakan su da nufi suci uban shi. shi kuwa karan ko
matsawa baiyi ba. daya yaje maka ma karan kulki
kawai sai gani sukayi ya bace bat. ai kuwa ido ya
raina fata. shima deeny da yake gefe yana kallo
abun ya bashi tsoro dan saida ya razana. suka
duba sama ko kasa basuga karan ba. ashe wannan
karan mai gonar ne ya tsafa su sunkai su 20 irin su
ashe dayan tafiya yayi ya kirawo sauran. ai kuwa.
suna tsaye sai ji sukayi wata irin guguwa ta tashi
sama……………https://m.facebook.com/groups/1232550283531628












→BANI NA KASHE TABA← PART 16
N@ BIGBOY isah
> suna tsaye suka ga irin karnu kan nan sai
zubowa kasa suke yi. ai kuwa da yan sanda da
deeny duk suka ari ta kare. sai gudu. su kuwa duk
karan da ya fado kasa sai ya nufe su da gudun
bala'i haka sukai ta tsere a cikin daji gudu kuwa
har sunyi sun fara gajiya daga sun waiga baya sai
suga wannan karnuka na biye da su da gudu.sunkai
mint 30 suna wannan mugun gudu. daba na wasa
ba gudun cetan rai sunsan in har suka bari
karnukan nan suka kamo su baza su bar ko da
kashin su ba. ai kuwa suka hango wani makeken
gida. auka nufe shi kuwa suna zuwa suka tura
kofar gidan suka ci sa'a ta bude su duka hudun
suka afka ciki suka rufo kofar. su basuyi tunanin ko
gidan waye bama a cikin dokar daji haka. su officer
anji jiki. duk sun yarda hulonan su a cikin gudun
nan nasu. kowa ya zauna sai haki suke sai huci. to
da suka huta ne fa suka ce ku tashi mu tafi suka
tashi ai Wannan dan iskan yaran duk shi yaja wo mana wannan bala'i ai tashi sukayi daya ya kama get din da niyar ya bude ai kuwa ina gamgam take ko motsi bata yi ogan cikin su yace me ke faruwa akace kofa taki buduwa yace baku da hankali gyara nan ya kama get din da kansa yaja yaja  kuwa kofa taki buduwa abun ya basu
mamaki sukayi sukayi kofar taki buduwa. ido kuwa
ya raina fata duk sukayi zuro zuro su basu karasa
cikin gidan ba kuma kofa taki budewa. haka suka
ce ta fanjama fanjam suka nufi cikin gidan duk su
hudun yanzu kowa ta kanshi yake ba maganar sa
deeny tsakiya.shi kuwa deeny ba haka ya so ba so
yayi ya tsere tun kafin su shigo gidan. to sai dai
daga ya juya sai yaga kare ya kusan kama mai
kafa. da yaga dai ba wajan tsira shi isa ya biye
musu har suka shiga gidan<
>
acan lagos kuwa aliyu ne ya nema Transfer da
yake shima police ne. a cewar shi gwara ya koma
gida kano zai fijin dadi. ai kuwa aka bashi Transfer
hada hutu ya samu na 1month. ya taho gida kano
da murnar shi. su maman deeny ne a tsakar gida
da ita da amina matar kawu kenan duk su biyun
sunyi jagwam jagwam suna ta tunani gobe idan aka
sama matsala za'a yanke wa deeny hukuncin kisa
fa. Idan ba'a gaskata zancan saba. sai sukaji sallama da sauri amina ta daga kai da
yake tasan mai wannan muryar aliyu suka ga ya
shigo ai kuwa murna duk suka amsa slm suka
tarye shi sai farin ciki suke sun ma manta da
damuwar da suke ciki..
Ni wllh alhj duk jikina yayi sanyi da jin zancan yaran
nan wllh gani nake kamar ba zai iya kashe halima
ba. maman halima ce ta fadi haka. wai ke wace iri
ce toh kin san manufar sa ne kika san ko dama can
ba santa yake ba so yake ya sace zuciyar ta daga
nan sai ya kaita yayi kudi da ita ko ai mazan yanzu
basu da gaskiya duk yan yau darane. ni kuwa nace
har kai ko. yaci gaba da cewa ai ba'a gane mugu
daga fuska ko daga dabi'arsa. ita dai maman
halima bata yarda deeny ya kashe halima ba. Domin tasan irin shakuwar dake tsakanin su har
zata kara magana sai ya daga mata hannun yace
dakata dan allah. kawai ya tashi ya shige dakin sa.
wayar hajiya ta dau kara. tana dubawa taga maman
Yazeed  ne. ta dauka suka yi gaishe gaishan su. nan
maman yazeed take cewa maman halima. gasu nan
zuwa.…………… https://m.facebook.com/groups/1232550283531628


mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group
bigboy
on-line 23.04 13:57
→BANI NA KASHE TABA ← PART 17
@N BIGBOY isah
tace gamu nan zamu zo dama shima yazeed din yana
da dan aiki da,zai yi a kano din. wannan karan har
da abban shi zamu zo. ko dan jin maganar
.maman halima tayi murna sosai da jin wannan
maganar. tatashi cikin farin ciki ta nufi dakin alhj ta
fada mai shima yaji dadi sosai. sbd ya dade bai
gana da yayan nashi ba. haka ranar akai ta girke
girke da soye soye. da yake shida
dan nasa kudi har sunyi musu yawa zance amma
duk kudin yazeed alhj bai san inda yake samo su ba
yasan dai albashin yazeed bai ko kama kafar kudin
da yazeed din ke facaka da su ba. alhj ya tambaye
shi ya tambaya har ya gaji amma saidai ya cemai
wai kudin salary sa ne da kuma busines da yake
dan juyawa da ita.amma alhj bai yarda ba sbd
kudin ba na wasa bane kuma lokaci daya kudin
akaga sun shigo masa. suna abuja amma a sati
sau biyu yake kwana a gida. idan suka ce ina yaje
sai yace wai harkar Businesses dinsu ne duka ya
koma kano. Misalin karfe hudun yanma anata jiran su maman yazeed amma shiru su alhj sanusi ne da matar sa zaune a parllo suna jiran zuwan su alhj bashir. Ko lfy har ynz basu karaso ba ai yaci ace sun karasa ynz kafin ta rufe baki wayan alhj yayi ring ya dauka alhj bashir ne yace mai suyi hkr baza su sama zuwaba sbd wani aiki da ya taso mai..<
>acan kuwa su anne ne suka fito sukaje wajan
maman anne. maryam ta gaida ta.ina ta amsa tana
zolayar maryam.wai yau ta kwana a bukka.
maryam tayi murmushi. anne tace mama ina abun
karin su gwaggon mu tafi maryam ta raka ni mu kai
musu. maman anne tace toh gashi ku kai musu
kuyi sauri ku dawo kuma kuzo ku karya. koko da
kosai ne sai tuwo. wai sune wayayu a garin shine
kokon aka zuba shi a cikin wani tshohn jog ne ja.
cike da koko. sai kosai a wata kula. towo da miya a
langa babba da karama. anne ce ta riko kwanan
tuwan da miya maryam kuwa ta dau koko da kusa.
suka fito suka kama hanyar gidan gwaggo suna
tafiya suna hira kamar dama can kawaye ne. fulani
kuwa sai kallan su ake ga anne da bakuwa yar
bunni. anne kuwa sai bude baki take. tana kallan
mutane tana dariya.ita kuwa maryam gaban ta sai
faduwa yake ta rasa dalili har sai da ta fadawa
anne. anne tace kodai gamuwa da yayan nawa ne
ya jawo haka kin san fa yayana kyakyawa ne.
maryam murmushi kawai tayi. a zuciyar ta tace
haba wa a kauyan nan har akwai wani saurayi da
zan so. suka dai ci gaba da tafiya anne sai zuba
surutu take.
gwaggo ce ta zauna kusa da halima tana cewa ya
jikin halima tace wllh da sauki sosai wai ni kuwa
har yanzu fa banga jikan naki ba gwaggo. gwaggo
tace ai yanzu zaki ganshi kin san yana wajan
farauta ne.assalamu alaikum. sukaji ance. suka
amsa. halima kuwa dayar muryar taji kamar ta
maryam amma da tayi tunanin me zai kawo
maryam nan sai kawai ta basar tace ba ita bace.
sai ji sukayi ance tsohuwa fito ga kokon ki. kina ina
ko dai kin mutu ne. anne ce tace haka. gwaggo
daga daki tace ai bazan mutu ba sai kin mutu ynz
yara suke fara mutuwa. sannan ne anne ta isa
kofar dakin tayi salm ta shiga ita kuwa maryam a
waje ta tsaya da kofin koko a hannun ta. yanda taji
gaban ta sai kara faduwa yake da ta matsa kusa da
dakin. anne ta kalli halima da itama kallan ta take
tace. gwaggo bakuwar yar burni mukayi halan.
gwaggo tace ke sai kin nuna kauyan cin naki a ko
ina ko. anne tace hb tsohuwa ai nima ga kawata
yar birni. ta mika hannu daya baya wai ta kamo
maryam sai taji bata nan.da sauri ta juya maryam
maryma. sai ta sama maryam a kofar daki
tsaye.anne tace haba maryam kamar dai ke ma
yar fulani ce. zomu shiga mana. kawo kokon.……… https://m.facebook.com/groups/1232550283531628


08096831009









→BANI NA KASHE TABA← PART 18
@N BIGBOY isah
tana shiga dakin tayi tsaye tana kallan halima.
itama halimar kasa yin motsi tayi ta kurawa
maryan ido itama. anne da gwaggo su kuwa duk
sun saki baki ganin kallo kallo da ake tsakanin
maryam da halima. gwaggo ce tace lafiya ko kun
san juna ne. sannan ne maryam ta gane ashe suma
su anne suna ganim halima da ta dauka ita kadai ke
ganin ta. maryma tace halima wai kece anan me ya
kawo.ki nan. halimar ma cewa tayi maryam me
kika zo yi nan. maryam ta karasa kusada halima ta
zauna a kan gadan da halimar take sannan
tace.aunty nayi mamakin ganin ki anan. halima
tace hmm kedai bari allah ne yayi da sauran
rayuwata ai. nidai tun lokacin da muna tare da dina
ya tafi sallah ya barni a mota. ni kuma ina nan a
mota nayi zuru zuru sai raba ido nake gani a bakin
titi mutane kuma duk an shiga sallah shima deeny
tuni yayi alwala ya kabara sallah. basai ganin mota
nayi an parka ta a kusa da ni ba wasu karti na gani
sun fito da sauri daya ya bude lid din motar dayan
kuma ya dauko wani pillow ga duk kan alamo dai
cikin wannan pillown akwai guba. cikin hanzari tayi
shirin fita ta dayan kofar kawai sai mutum ta gani a
tsaye da pillow a hannun sa kafin tayi yin.kurin iho
tune ya hada mata baki da hanci ya danne da pillow
dayan kuma ya ririke hannun ta kuma ya danne
mata kafafu saboda shure shuren da take can
sukaji ta yi lakwai bata iya motsi baban naku mugu
sai cewa yayi kai kumurci saketa mana bakaga ta
mutu ba ko gawar ma kashe ta zakayi.dai dai nan
suka kula anyi zaman tahiya a masallaci za'a salam
ce ne da sauri suka kukule kofofin motar suka ruga
da gudu tasu shi kuma ogan nasu yana ciki yana
jiran su aikuwa suna shiga yaja mota . nidai tun
daga lokacin ban farka ba sai a nan gidan. gwaggo
da anne duk sun tausaya mata. suna tunanin to
waye yazo binne ki tace nima dai ban sani ba itama
maryam tayi jum kadan sannan itama ta kwashe lbr
ta duk ta gaya musu sukayi mamaki sosai.
sallam sukaji anyi duk suka amsa. halima kallan
saurayin take azuciyar ta tace wannan da alamo
shine wanda ya cetoni. ita kuwa maryam kanta a
kasa ta kasa dagowa ta kalle shi ma. sakamakwan
gaban ta da taji yana faduwa. cewa yayi gwaggo
ina kwana ya jikin bakuwar gwaggo ta amsa. tace
bakuwa gatanan har ma ta warware har hira muke.
anne ce ta durkusa tace yaya isah ina kwana.yace
lafiya lau ya mamana. maryam jin anne tace yaya
da sauri ta daga kai tana kallan sa taga ita yake
kallo shima. ai kuwa a tare suka kauda
kai.sakamakon wani mumunan faduwar gaba da
sukaji su biyu. wai me hakan ke nufi daga kallan
yarinya gabana ya fadi. nida naga yan mata kala
kala. iri iri. duk ina kura musu ido amma ban taba
jin irin haka ba sai yau isah ne ke fadar hk a
zuciyar shi. maryam kanta a kasa tace ina kwana
yaya isah ya dan kalle ta sannan yace lafiya kalau
yace sis wannan fa ya tambaya annee. annee tace
wannan sunan ta maryam jiya muka hadu da ita
yan daba sun biyo ta allah ya kawo ta garin mu a
dandali muka hadu kuma a gidan mu ta kwana.
bayan anyi shiru daga can halima tace yaya ina
kwana ya amsa lfy ya karfin jikin tace jiki da sauki.
yace to allah ya bada sauki amma baki bani lbr
abunda ya faru da ke ba. halima ta kwashe lbr kaff
ta fada mai. ya girgiza kai alamon mamaki. sannan
kuma anne ta ci gaba da bawa yayanta lbr maryam
sai da ta fada mai duk tun daga fitowar maryam
daga gida har zuwa sace ta da tserowar da tayi da
haduwar su duk ta fada mai komai yayi jum kadan
can sai yayi wupp! yace mutum nawa kika ce ya
kalli halima tace uku.ya juya kan maryam yace
kema uku ko. maryam da kanta ke a kasa ta dago
ta kalle shi da kwala kwalan idanon ta masu daukar
hankali tacje eh su uku ne. ..........   Washhh har naji dadi halima bata mutu ba kufa ???? ."










→BANI NA KASHE TABA←




Part 19



N@  bigboy isa






Yace tabbas mutum daya ne yasa ayi muku wannan aiki domin kuwa la'akari da labarin ko wacce daga cikin ku amma  ba wani wanda kukawa laifi kuwa ko wulakan ci ko maka mancin hk duk suka girgiza kai alamun babu yace to alhmdulilah ynz dai tunda allah ya tsalllakar daku ku biyun yanzu abunda yafi shine zamu jira kudan huta kafin mu tatara mu tafi birni can wajan iyayan ku domin kuwa bamu san wane hali suke ciki ba a halin yanzu. Duk wannan zancan da yake yanayi yana satar kallan maryam lokacin nema ya dan gaskata zcyar sa a bisa zargin da yake akan maryam. Gwaggo tace gaskiya ne allah ya maka albarka sannan yace gwaggo ni zan fita ya mike hade da kallan wajan da Maryam ke zaune ai kuwa kamar hadin baki suka hada ido wani zazafan faduwar gaba sukaji a tare cikin su kowane ya rasa daliln haka.nan dai ya fita ya barsu sai hira suke shi kuma ya nufi gidan su wato gidan su anne domin haka yake duk safiya sai yaje ya gaishe da iyayan sa ( hmm iyaye ba abun wasa bane ya kamata mu lura mu kyautata musu wani zaka same shi shi gani yake gaida iyayan sa ma kamar wani zubar da class ne alhalin kuma wannan dabi'ar banza ce bata kirki ba allah yasa mu gane ameen) yaje yayi sallama aka amsa ya kuwa iske su a daki suna hira ya tube takalmi ya shiga dakin ya ce ina kwanan ku suka amsa ya gwaggo inji maman anne yace duk suna lafiya wllh baban yace kaga munyi bakuwa ko eh baba nima dama ina so in gaya muku jiya bayan  na fita farauta da dadare sai na biya ta garka to kaiwai sai naga mutum yana rami na dauka barayi ne kawai sai na far masa na bisa ina harbi amna allah bai bani saa na same shi ba ya shiga motanshi ya gudu to ina dawowa wajan kuma sai na iske mutun ashe wai mutum yazo binne wa dana taba kawai sai naga macece lokacin kuma anyi sa'a ashe wai dogwan suma tayi kuma lokacin da naje ta farfado kawai sai na dauke ta na kaita gida ynz dai tana can ta farfado  ta sama sauki sosai sudai kawai gyada mai kai suke jin abun sukayi kamar al'mara  badan mgnr daga bakinsa take fitowa bama da wanine ke fada musu cewa zasuyi karya ne. yaci gaba da cewa umma kuma wani abun  mamakin shine da yarinyar da ta zo nan gidan da kuma wacce na tsinta sun san juna wai kawaye ne ma  maman anne ta rike baki tace sarautar allah kenan shine yayi ikon sa a kansu. sannan tace to ai yanzu kamata yayi muje can gidan gwaggonka domin asan mafita domin kuwa iyayansu zasu shiga wani hali. baban anne yace to kuyi gaba nima  gani nan zuwa ynz ba irin tashi hankali da kuma fargaba da maman deeny ta shiga ganin har an kwana kuma ba labarin su deeny har yanzu basu dawo ba domin sai zarya take police. su ma haka yan gidan su halima ya daya kenan ita kadai gare ta yanzu idan ta mutu ya zatayi gashi yanzu na daima haihuwa hawaye ne zafafa suka  kwaranyo a idanonta can kuma sai naga ta tashi ta bude wardrobe ta dauko hijab  tasa ta fito ta ko ina zata oho haka ta fita rai a bace ko ta kan driver bata bi ba domin gani take bata lokaci ne ta fito haka mai gadi ma ko kallo bai isheta ba balle ma ta fada mai inda zata napep naga ta tsaida..... ..........       


big boy kune 










  😫🔫  BANI NA KASHE TABA  😫🔫




Na 👑 king boy👑



Part 20






Tana tsayawa ta shiga tace muje nan baya zaka kaini ranta a murtuke… bata zame ko ina ba sai kofar gidan su kawun deeny wato dai wajan mamar deeny ta zo. Tafito ta nufi cikin gidan ganin bata da niyar bashi kudin sa ne yace hjy kudin fa. Jirani haka tace mai ba tare da ta juyo bama. Suna zaune Suna zaune suna jimami sai ji sukayi. Murya kamar daga sama ku fiddo min ya'ta tana hawaye dan allah ku taimaka min ku bani yarinya ta ita kadai na mallaka sai hawaye suka fara zarya gaba daya hankalin su ya tashi bama kamar maman deeny tace ga kujerq zauna mana aa ba zama nazo yi ba nidai kawai ku taimaka min ku fiddo min da di'yata mamar deeny kasa cewa komai tayi daga haka kawai kuka take abubuwa sun mata yawa ko abinci kwanan nan biyu bata iya ci duk ta rame. Aliyu naga ya fito daga dakin sa wanda yana jin duk abunda ke faruwa yazo gaban maman halima ya kalli maman deeny yace wannan ita ce mahaifiyar yarinyar? Kai kawai ta iya daga mai alamun eh ya maida hankalin sa ga matar wacce kuka yaci karfin ta sai sharar hawaye take da hijab dinta ya yi kasa da murya sannan yace inaso ki kwantar da hankalin ki ki saurari abunda zan gaya miki pls ki natsu ya dauko wata kujera ta katako wa ajiye sannan yace zauna ba gardama ta zauna ita da farko da niyar masifa taxo amma harga allah yanda ta iske su suma gidan gaba daya ba wani walwala shi yasa taji duk jikinta yayi sanyi. aliyu yace to da farko inaso ki natsu kiyi tunani sannan zan gaya miki wannan maganganun ne bawai dan baki sani ba aa kawai dan tunatarwa yace ki san cewa komai mukaddari ne daga allah duk abunda ya faru da mutum to daga gare sane alkhari ko makaman cin sa saidai abunda wasun mu basu gane ba shine a lokacin da allah ya sauko da alkhairi ga mutum sai yay ta jin dadi wani ma baya godewa allah domin gani yake kamar wayansa ne ya kawo mai wannan alherin. gaba daya maman deeny da maman halima da kuma ita kanta amina wato maman sa duk sunyi shiru shi kawai suke sauraro. yace to idan kuma allah ya jarabci mutum da wata masifar kuma sai mutu kaga duk ya rikice a nan ne ma zai tuna da allah hmm shi kuma allah zaima wannan abun ne dan ya gwada iya imanin ka..... nandai yata mata nasiha itadai tayi shiru sauraran  sa kawai take.yace to ina so ki dauki wannan abun a matsayin kaddara sannan ki dage da addu'a domin addu'a itace maka min mumuni yace ke naki mai sauki ne ma domin ke kin fara cire rai ga yarki domin ance ta mutu ya nuna maman deeny yace kinga maman  sa nan itama da shi din da kuma maryam wato kanwarsa duk ba daya daga ciki domin ita maryam tun ranar da abun ya faru ta tafi islamiya bata dawo ba har yau shi ma dini kuma haka domin suma basu dawo ba daga binciken da suka tafi  mamar deeny wasu zafafan hawayan ne suka kubuto mata wanda ita kanta hjy khadija wato mamar halima saida ta tausaya mata sannane ma ta san wai maryam bata dawo ba yace ynz abunda za'ayi shine kiyi hakuri ki koma gida kici gaba da addu'a domin lamarin nan sai addu'a dai. jiki ba kwari ta tashi ta musu salama duk a kunyace domin yanda ta shigo musu da fari tana fita da tarar da dan adaidai tar nan inda ta barsa ya fiddo waya sai chat yake abunsa shi kam yama manta da wata yake jira chat yayi dadi ta hau tace mayar dani inda ka dauko ni. yayi mamaki shima yanda yaga matar da farko cike da damuwa ynz kuma gashi ta fito ba kmr dazu ba ya tuka ya maida ita tana sauka bata tsaya tambyar ko nawa ne kudin ba ta zaro 1000 sabuwa dall ta mika mai domin tasan kudin sa baikai hk ba ta wuce zata shiga gida yace hajiya chanjin fa tace ka rike ba tare da ta waiwayo ba dadi ne ya cika shi shi kuma domin riba biyu ga ya huta kuma ga kudin da ko lokacin aiki yake bai isa ace dubu ta shigo ba yaja adaidaitar sa yayi gaba tana shiga gidan sai  wayarta tadau kara tana dubawa taga hjy saratu ce take kira ta dauka suka gaisa nan take tmbyar ya lbrn halima tace abundai gashinan sai addu'a nan hjj saratu take gaya mata suyi hkr da basu sama zuwa ba amma ga yazeed nan zuwa yau yau....  ...........




A CAN BANGARAN SU DEENY KUWA.........






ISAHN ♥ KUNE








  😫🔫  BANI NA KASHE TABA  😫🔫




Na 👑 king boy👑



Part 21


.

CIKIN gidan suka nufa suna waige waige yana yin gidan ya fara furgita su domin ko motsin basuji ba wata kofa ce katuwa wacce akayi da zinary a sukazo kofar dakin sukayi curus kowa yaki yarda ya fara taba kofar ogan ya kalli deeny da jikin sa ke rawa yace kai zo ka bude mana kofar nan dan uban ka. Haka ya taho yana makyarkyata kamar ya kama kamar kuma yaki saidai yasan ba yanda ya iya
Wata zuciyar tace mai kai koma fa kun kubuta daga gidan nan to ba makawa kashe ka za'a yi domin banda wannan hujar ba wata tunda anzo ba'aga ko ramin ba kaga kuwa ba makawa kashe ka za'ayi sai yaji duk tsoro ma ya fita a ranshi. Ya rufe ido yayi yan addu'o'i sannan ya sa hannu biyu ya tura kofar  da yake kofar mai hannu biyu ce kamar get gani sukayi kofar ta bude kai tsaye Suka nufin parllo suka fara salama shiru basuji ko motsi ba hakan yasa suka kutsa kai sukayi cikn. Katan farllo ne tan gameme yasha ado kujeru ne jere birjik a parllan ga kuma can wasu dakuna ba adadi a jere sai kalle kalle sukeyi domin dakin ya hadu sosai durum wuta sukaga ta dauke hade da wata shu'umar dariya hahahaha muna maraba da ku yau abinci har gida hhhhhhh dadai zuwa mukeyi mu kamo da karfin mu ko musa sihirin mu mu kama amma yau muna maraba da sauyin da yaxo mana cikin wannan masarauta hahahahaa kuma sai sukaji tsik dariyar ta dauke wuta kuma ta dawo a kame na gansu waje daya ko wanne cikin su sai karkarwa yake deeny kuwa da yake baya wasa da addu'a tun da yaga wannan al'amari ya dukufa karanta →ayyatul kursiyu← ( yan uwa mu bar wasa da addu'a duk a binda kaga zai firgita ka saka allah a ranka ka fara addu'a zakaga dace sannan tsoranka zai fita allah kasa mu dace ameen) can kuma sai hasken ya fara ya kawo ya dauke can kuma sai gaba daya dakin ya zama ja jawur wata kofa sukaga ta bude wasu karti ne ke futuwa daga ka gansu kasan ba imani ko kadan a ransu gasu bakake duk ba riga sai Ja jayan wandu na a jikin su da kuma jan kyalle a kansu sun dadaura.kowa ta kansa yayi dukan su kofa suka nufa da gudun su kowa na ta kansa wutar dakin ta dauke dub..   can jimawa kadan sai wutar dakin ta kawo kowa ganin sa yayi a hannun kato guda hankalin su tashe kowa sai fizge fizge yake deeny ne kawai baya fizge fizge kasan cewar shi tuni ya sadaukar da rayuwar sa a zuciyar sa kuwa addu'a  kawai yake wani tsoho ne ya fito kanaa duk furfura cikin fararan kaya idanunsa jawur da  alamun dai shine shugaba a wannan gidan  hahahaja haka ya taho yana dariyar mugunta yaxo gaban su daya bayan daya yana kare musu kallo sai fizge fizge suke deeny kadai ya gani a nutse yaje gaban sa ya tsuguna tsayin su yazo daidai yace yaro nan fa gidan mutuwa ne nan gidan shan jini a ci nama ne nan gidan a tarihin sa ba wani mahaluki da yake shigowa ya fita da rai in ba dan kungiya ba amma kai me yasa naga kamar baka damu ba alhalin kasan mutuwa zakayi 
deeny ya dago kai wanda har lokacin gabansa faduwa kawai yake da ya hada ido da mutumin nan duk sai yaji tsoro ya fita a jikin sa ya samu kwarin gwewa. yace hmmm me kake tunani ne da kake fadar wannan mgnr ko dan banyi mamaki ba domin kai ba imani a zuciyarka bana tunanin kana da ilimin sanin allah da har zakasan shine mai kashewa mai rayawa ba kuba. hakika maganar deeny ta bata masa rai. ya daka masa tsawa kai yaro ni kake gayawa wannan bakaken maganganun ya kama habar deeny ya zaro wata wuka ya dora mai a wuya yace sake fada mgn daya in baka sheqa lahara ynz ba kuma jinin ka zamu sadaukar da shi ga gunkin mu sanan namanka yan kungiya ne zasu cinye hahahahah mgnr da deeny ya fada itace ta tsaida shi daga dariyar hade da jin wani mugun bacin rai kamar xuciyar sa zata kone. kai jahiki ne wannan mgnr ce ta fito daga bakin deeny wanda har ynz wukar ce a wuyansa. can kuma sai ya tuntsire da dariya hahahah i like this boie ina san marar tsoro irinka da zaka shigo kungiya mu da ka huta yaro da ka more dadin duniya kuma kaci arziki ka barsa hatta jikokin ka ma bazasu yi talauci ba. tirr tirr da wannan muguwar kungiya taku da zaka gane alherin lahira shine yafi dacewa da ka nema jindadin duniya aikin banxa ne....... waya tayi ringing wani kato ya mikowa ogan wayar sir bad boy calling ya amsa wayar ya kara a kunne yana kallan deeny hello bad boy daga can kuma hw ar u dady 5yn dad i will come 2 kano 2day wow am hppy  bad son kafin kazo kuwa zan tana dar maka baban abun tarya. tnx dad bye. ok bad. tashi yayi daga wajan deeny yake fadawa wannan kartan bad boy na hanya dan haka dole a tanadar masa muhimmin abu ya kalli yan sanda wanda duk a tsure suke yace waye oga a cikin ku waye babba? kowa ya nuna dan uwansa ogan ma na gefan sa ya nuna suka kama bararabi. tsawa ya daka musu nace waye babba yana karkarwa ya daga hannu yallabai nine ku kawo min shi nan. saida akazo gaban deeny dashi sannan yasa wasu kartai suka danne wannan ogan yan sandan yasa wuka wuluk sai ga kai a kasa............ king boyn kune










😫🔫 BANI NA KASHE TABA 😫🔫.




  Na big boy isah



Part 22






Gaba daya sauran yan sanda sun kidime sakamakwan basu saba ganin kisa irin wanan ba deeny kuwa ido ya lumshe hade da cewa ya allah. Ya daga kai sama. Hahahahaha tshon ya fara dariya suma kartin nan gaba daya sai suka kama dariya can kuma sai yayi shiru kamar hadin baki suma kuma duk sai sukayi tsit sannan ya nuna wasu karti hudu yace ku dauki wannan naman ya nuna ogan yan sandan nan kuje ku gyarama oga domin yana nan tafe cikin yan secondna tuni sun dauke sa ya dubi su deeny yace  kuma duk waka zamu muku domin ba mai shiga gidan nan ya kubuta kuma baza'a fara a kanku ba dan haka sai ku shirya yana gama maganar ya juya ya nufi wani dakin har zai shiga ya juyo ya kalli wani kato daga cikin kartan nan yace ku kaisu dakin ajiya ya juya ya shige dakin .....



su anne ne zaune gidan inna sai tadi suke su ukun kmar dama kawaye ne gwaggo tace ai gwara ku tashi ku tafi can gidan ku ta kalli anne tunda kinga yamma tayi anne kuwa cijewa tayi wai ai ita bata so a rabasu da halima duk dadai tare da maryam zasu koma tace inna me xai hana mu kwana a nan ynz inje in kawo mana abincin rana da dadare ma haka inje in kawo ina tace to kwantar da hankalin ki tare da halimar zaku tafi can ku kwana uwar iyayi har zaki fara kawo mana kabli da ba'a di  ba yanzu kuka sha fura ba har wani abinci rana kuma za'a ci da sauri su maryam suka kalli kaka. kaka fura ce abinci rana kuma cewar maryam. kaka ta rike baki ohh ni ya'su  yanzu bayan furar nan  har wani abinci kuma za'aci. anney tace hmm kunga ku kyale ta ai tsohuwa ce ita ta kusan margayawa shi yasa bata iya cin abinci da yawa amma ko ni nan ai cikina ba komai nake jinsa. su duka suka hau dariya halima tace ai ni fura dan marmari kawai nake shanta ba dan koshi ba. kaka tace kundai hade baki ko to ai sai ku tashi ku tafi can gidan kuci abinci ni dai na koshi furar na ta ishe ni har gobe da safe duk suka zaro ido gobe fa. Anne ce ta tashi oya standup following me tayi gaba su kuwa dariya sukayi turancin yar rugga....

tafiya suke su kunya suke ji duk jikin su ko gyale babu duk ba wacce ke da gyali a gunta ga mutane sai kallan su ake ita kuwa anney sai wani bun kasa take ita wai with yan bunni haka sukata tafiya duk garin ba mai kyau anney saka makwan gata fara da kyan diri hadee fuskar ta yar doguwa ma daidai ciya duk da yake ba duguwq bace sosai amma kuma ba gajera ce ba duk da su maryam yan burni ne basu saba da wahala ba ba abunda zasu nunawa anney saidai ma ta nuna musu da yake yar fulani ce
Tafiya suke suna ta shiririta sun biye wa anne ta saya musu wannan ta saya musu wannan sai washe baki take tana tare da yan bunni. A haka har suka karasa suka iske maman anne tuni ta dafa abinci su kawai take jira da yake tanada yar sauran shinkafa itace ta idasa dafewa suka shigo da salamar su ko wacce da murmushi a fuskarta haka anne taje ta dauko musu tabarma roba wai a cewar tayan burnine ba tabar mar kaba za'a basu ba. Suka zauna a ka zubo musu a tran silva suna ci suna hira salama sukaji. Gabaki daya suka amsa hade da kallan kofar shigowa  da sauri maryam ta kauda kai ganin mai salamar ba wani bane isah ne rike da zoman daji dayan hannunshi kuwa ya riko kwari da gwafan shi...................oooppppps




King ne ♥










BANI NA KASHE TABA 😫🔫.




  Na big boy isah



Part 23












Maman anney ta fito da mamaki a fuskarta dannan sannanka da zuwa yau kuma kane a gida da rana haka abunda bakayi.ya sunkuyar da kai wanda ya kara bayana kyan fuskar sa tare da cewa uhm uhm..... Yama rasa me zaice ya kama in ina gaba daya suka kama kallan sa maryam ce kawai taki dagowa domin in suka hada ido wani abu take ji na daban da ta rasa minene. Cansai yace ummana dama wannan na kawo muku ya daga xomo tare da nunashi.tace hmm dama kana kawo mana xomo a haka ne ai sanin da nayi saika babake ka gyara kake kawo mana yadan sosa kye kuma dama inajin yunwa ya kalli gurin tukunya an gam? Maman nashi ita duk mamaki ya cikata tace nema waje ka zauna bari in kawo ma. Haka ya samu wani dan turmi ya zauna.


Yanayi yana satar kallan maryam a zuciyarsa yace shin wai yarinyar nan ko dai yar fillo ce ji tsabar kunya taki kallo na ma hmm yarinya kenan ai wllh tunda kika riga kika harbo kibiyar so ta caki zuciyata ba yanda za'ayi in barki wata zuciyar tace sbd me? Kana santa mana..... Duk zancan zucin da yake idan sa na kan maryam suma da suke gefe suna cin abincin su. Kai kai dan nan maman sa ce a tsaye ta kawo mai abincin firgigit ya xabura ya karba. Me kake tunani haka meke damunka tabbas ta gane me yake kallo domin tun sanda ta kawo mai abincin taga idansa na kan maryam. Yace umma ba komai wllh kawai ina dan nazari ne. Ta juya tare da cewa to allah ya kiyaye. Anney kuwa da hankalin ta yana kan su isah tuni ta gane abunda ke faruwa tayi murmushi a zuciya tace wato yaya isah anga yar burni......   Yazeed ne ya shigo da motar sa mai gadi yayi saurin budewa da yake ya gane ko waye. Gadan gadan gunda aka tanada domin park mota ya ajiye ta karamar mota ce kirar 407 ya tsaya tare da fitowa ya ya nufi cikin gida  maman halima na parllo ta kunna kallo taji shigowar sa ai kuwa cikin far'a ta tare shi. Tare da kirawo yan aiki suje su dauko mai kayansa a moto. Haka suka zauna farllo suka gagaisa sosai sannan ya tashi ya nufi dakinsa wanda dama nan aka tanadar masa idan yazo nan yake zama yan aiki  ma sun sani domin can suka kai mai akwatin sa da sauran kayansa. Maman halimar tayi mamaki mutuka da yazeed bai tambaye ta ko ince jajanta mata a kan haleemar ba saidai kuma kawai ta basar tace amma kuwa indai rikicin da sukayi da haleema ne har ynz abun ya tsaya mai a rai har ya gagara min mgnr ta gaskiya bai dai2 ba hk dai tata sake sake< 

Abunda ya hada su fada wancan zuwa da yazeed yayi>




Oooopppppppssss




King boyn kune











BANI NA KASHE TABA 😫🔫.




  Na big boy isah



Part 24








YAZEED dai ya kasance baya san surutu idan ya shiga dakin da yake sauka a gidan su haleema ba ya bari kowa ya shigar mai daki kuma sai yayi shiru ko motsinsa ba'a ji. Wata rana waje jan karfe goma na safe duk anyi Brkfast kowa ya watse ya kama harkar gaban sa ba sauran abinci sai na yazeed gashi kuma yaki zuwa ya dauka yaki fitowa a daki halima abun ya bata mamaki ganin 10:30 shayin zaiyi sanyi da sauran kayan brk din bai fito ba ita dai tana nan tana ta danne danne a waya ta leka can ta leka can nan har ta kira deeny suka fara waya. Har suka gama ta duba agogo taga 10:40 har zataje ta dauko plast ta juye mai kuma saidai ta fasa.a zuciyar ta tace ba'a shiga dakin ka ko to wllh ni yau sai na shiga saidai in kashe ni zakayi kayi ta dauki kayan break din ta nufi dakin da yazeed yake. ta yi nifin kwankwasawa buga hannunta keda wuya taji kofa ta bude a sanyaye ta saka kafa kamar marar gaskiya tsakar dakin ta tsaya tana yan dube dube ganin yana ban daki ta ajiye mai kayan break din a tsakar daki can wajan waige waige ta hango wani abu kamar kwaran gwal sai dai a lulube yake tashi tayi a hankula ta nufi wajan mika hannu tayi da niyar ta cire abunda ya lulube wannan abun wata irin tsawa taji an daka mata da sauri ta juyo yazeed ne ya fito daga toilet daure yake da tawul ga dukan alamu ma bai gama wankan ba haka ya fito sakamakon jin an shigo dakin domin ruwa kawai ke disa a jikin sa ita abunne ya burgeta ta tsaya tana kallan sa yanda ruwa ke bi ta yalwacacan kirginsa ga gashi lip lip abun gwanin sha'awa ji take kamar taje ta rungume shi. Saukar marin da taji shi ya dawo da ita hayyacin ta taaatssss baki da hankali  ne ke wawuyar ina ce uban wa ya kawo ki nan  bana hana kows ya shigo min room ba kuma u know shine zaki shigo min daki get out ita kuwa duk ta wani sa hannuwa ta rufe kumatun ta biyu sakamakon marin da ya sakar mata uban ihu ta saka radadin zafin mari ganin batada alamun tafiya yasa shi kama hannunta da karfi yaja ta ya kaita out tukun ya dawo ya saka key ya kulle dakin. sa kuka take sosai  hakan yasa mamanta taji ta taho da sauri lafiya lafiya kuwa haleema subuhanallah me aka miki kike kuka bata iya cewa kumai ba domin koka yaci karfin ta haka ta fara zage zage tana kuka tana allah ya isamin wai momy daga na kaimai kayan break cikinn kuka take maganan mum dinn ta shiga lalashin ta tana cewa kiyi hakuri mana keda ba yarinya ba kuma kinsan cewa ba'a shigar mai daki me ya kaiki shiga. Ta kalli umman nata ido duk hawaye mum abincin sa fa naga zai huce na kaimai. To me yakai ki yanzu dai ai gashi kinjawa kanki mum din tayi gaba. Kare fashe wa tayi da wani saban kukan me hade da shagwaba mum bazaki ce mai komai ba tana bubuga kafa. Toni me zance mai ai ke ce kika jawa kanki. Kofar dakin taje ta fara aika mai sakon nin zagi kala kala. Haqiqa yaji haushi haka ya zare bel ya bude door ya nufota a guje................... Nima gudun wa nayi .lolx











King boy ne












BANI NA KASHE TABA 😫🔫.




  Na big boy isah

.

Part 25



.


Note.. 

A zancen  gaskiya dole inyi jinjina a  gare ku masu bibiyar novel dina Dubun godiya a gare ku da bibiyar BANI NA  KASHE TABA duk da nasan ba wani dade gare sa ba amma a haka kuke hkr dani kuke bibiyar sa 😀 ina jin dadin haka  amma ku san cewa mai hakuri wata ran xai dara domin wannan shine first novel dina kunga kuwa sai slow but da sannu sannu  yaro ke girma dan haka ku kara hkr inda nayi ba daidai ba luv u oll 😘😘😘

.
.
.

Haka sukaita zagaye parllon yana ta zane tana kuka da ihu sai hajiya ce ta raba to tunda ga wannan ranar kuma ba maiwa wani mgn tsakanin ta da yazeed but tasha duka.... Wannan kenan


... Yana shiga dakin ya cire kayan jikinsa ya shiga toilet ya hada ruwa sannan yayi wanka ya fito ya feshe ko'ina na jikin sa da turare sannan ya kama shafa wani abu wanda bansan ko me nene ba ga alamu dai abun nada wari domin turaran ne ke hana jin warin jeans yasa tare da wata black shirt ya taje gashin kansa sannan ya dau wayoyin tare da car key dinsa ya fito hjy ya iske a parllo mum har ynz dad din bai dawo ba? Yace yana dan murmushi eh wllh kadai ga har ynz gashi yamma ta fara yi ok mum zan danje nan  wato maman hallema da yake mum yake ce mata. Haba yazeed kaima kasan hakan bazata faru ba ga abincinka can fa a dinner an hada maka kuma kace zaka fita ko abinci baka ci ba shin wai inama zaka? Inda yaji kansa ya daure haushin kansa ma yaji  da ya tambaye ta can kuma ya dago kai au wllh zanje gun friends dina ne domin tun kafin ynz suna ta called dina naki dagawa shine nake sauri in fita kuma bana jin yunwa ynz wllh....

To shikenan a dawo lfy in ka dawo kaci.

Fita yayi yaja motarsa a guje ya dau hanya ko ina zasa oho......



Haba mum deeny kamar yarinya ki dinga kuka haka  addu'a ne ya kamace mu b kuka ba dan allah kiyi hkr aliyu ne yake bata hkr ita kuwa sai sharara kuka take mai matukar cin rai da ban tausayi ga wanda duk ya gani  haba aliyu taya ta wace hanya ce zan iyayin shiru ai ko nayi niyar hakan bazai yuyuba zuciyata kuna take a ko wane lokaci idan ba kukn nayi ba bana ma jin dadi. Sanan ta hau wani saban kukan wanda saida ta cika dan karamin parllo. Cikin kuka take cewa miye amfanin rayuwa ta in ba wannan yaran me amfanin tama. Ya salam yace hb mum da girma ki fa kuma kinsan kaddara. Wqce irin kaddara ce wannan da zta rabani da yarana iyee wace kala ce... Nan dai na barsu tana kuka abun tausayi ana rarashinta....



Hanyar wani kasurgumin jeji ya nufa gudu yake kamar me baya da niyar tsayawa haka yata lumawa cikin daji da motar sa  wajajan 6:00 ya isa kofar wannan kata faran gida wato inda su deeny suke bisa mamaki yn zuwq kofa ta bude ya kutsa kai ya sama waje yayi park. Wani sashe da ban ya nufa a cikin gidan ya shiga wani room sai gani nayi yazeed ya canja shiga wato ya cire kayansa ya saka wasu jajaye ne riga doguwa tare da wani jan wando.............


By

Bigboy isah











🔫.BANI NA KASHE TABA 😫🔫.



5 star's ✨✨ online writer's association 👌


  Na big boy isah

.

Part 26











Sannan ya  daura wani jan kyalle a goshin sa saidai nasa ya banbanta da na sauran wancan kartin shi zai tabbatar maka cewa shima babba ne a kungiyar sannan ya dawo ya nufi wannan kofar dakin ai kuwa yana nufar kofar ta bude sannan ya shiga. Gani nayi duk wannan kartan sun wani jeru layi layi sunyi sahu sahu face to face ta tsakanin su ya wuce duk wanda yazeed yazo saitin sa sai ya durkusa kasa dan kwasar gaisuwa. Wannan tsohun na hanga can kan wata kujera ya hakime ga wani dinner table a gaban sa duk kujeru ne a zagaye da tabal din sannan sai wata kujerar mai kama da tasa a kusa da tasan kai tsaye yazeed ya wuce dayar kujerar ya zauna sannan ne naga suma manyan cikin kungiyar sun zo duk an zazauna kowa da plat a gaban sa abun dake cikine zaisa idan ka kalla sau daya baza ka kara ba sasan jikin mutum ne kala kala a ko wane plat ba kyan gani welcome my son inji tsohon juyawa yayi ya kalleshi hade da cewa thank ya sannan tsohon ya

Ya tashi yana wasu gwalan gwalan tun tsafin sa sannan yace muna maraba da babban yaro na kuma shugaba magajin wannan kungiya wato yazeed bad man ya dora da cewa kun sani cewa a cikin mu ko jikokin dan kungiya bazasu yi talauci ba bazasu taba sanin miye babu ba kuma baza mu yi sasauci ga duk wanda ya bujirw ma umarnin mu ba sannan ku sani dole ku kula da dokokin kungiya sannan ya juya ga yazeed yace dodon mu yana bukatar jini kuma daga gareka wato a cikin family naka dole ka bamu jininn ka domin tun farko kayi alkawari cewa a wannan sheqarar ne zaka bayar chan kuma cikin dakin ajiya wato inda aka sa su deeny sun matukar gala baita yunwa ma ta ishe su gashi anki kawo musu abinci sauran kuwa wannan yan sandar biyu tuni sun gala baita sun sha kuka kamar ransu  zai fita dole suka hakura sukayi shiru domin ba mgni kukan ke yi musu ba. Deeny ne ya tashi ya nufi kofar futa sakama kwan mgn da yake ji sama sam lekawa yayi... Ta wata yar kofa da sauri ya dago ya dan kama baki alamun yana so ya tuna wani abu a ina yasan waccan fuskar kamar ya taba ganin ta kunne ya kafa yana saurare me suke cewa.. ..



Yazeed ne ya miki yayi gyaran murya a matsayina na mataimakin shugaban mu kuma babana gashi a zaune ya nuna wannan tsohon. Inaso in muku bayani wato dan takaitacan tarihina domin kusan cewa a harkar nan ba imani idan kanada imani bazaka ci muriyar mu ba...


Ni dai na kasance fuska biyu ne domin idan ka ganni a gari bazaka taba cewa ni mugu bane yanda nake al'amura na sakin fuska kyauta da sauran halaye masu kyau.  Ina so ku sani yan matan da na kawo nan aka hallaka sun fi a kirga kuma duk a matsayin saurayi nake gare su abunda baku sani ba shine duka ba wacce mahaifan ta suka sanni hatta anguwa sai naje nesa da tamu sannan nake yin budurwa ku sani cewa yan matan yanzu ba ruwansu da SAN GASKIYA kawai sudai abun hannunka suke bukata laifin iyaye kuwa da suke barin yaran su wato mata suna fitowa zance alhalin basu san saurayin ba abunda ya kamata idan yaro yazo gun yarka to kace mata gobe in yazo ku shigo mu gaisa. Ta haka zaka dan rage mayaudara a cikin masoyan yarka....


Ya danyi shiru tukun yace karfa ku zata wannan nasiha ce no ni da kuke gani ba alamun imani ko tausayi tare dani ni na hallaka haleema ya fada tare da kawarta maryam sakamakwan tona min asiri da suka so yi.....


Gaban deeny ne yayi mumunar faduwa sai ynz ya gane yazeed din sakamakwan sau daya ya taba ganin sa haka ya dafe kai da yake sara mai da karfi  yanzu yana nufin ya hallaka min merry dina no nio no haleema na da gaske kin mutu kaaaaai ban yarda ba karya kake karya kake ganin zasuji yayi saurin control din kansa ya natsu sai hawaye sharrrr!  Can ya sake kafa kunne dan jin me yazeed ke cewa...


Sannan ina so in fadawa kungiya cewa lalai ni mai cika alkawari ne dan haka naba kungiya babana mahaifina a ynz ranar Friday zan kawo shi domin baya garin nan amma tabbas nasan yanda xanyi in kawo shii wannan babbar kyauta ce nawa kungiya... Gaba daya suka fara clapping.........................


Allah ya bamu yaya na gari karka bamu mai halin yazeed 👏🏽👏


By king boy isah

https://m.facebook.com/groups/1232550283531628
















🔫.BANI NA KASHE TABA 😫🔫.



  Na big boy isah


.  *DEDICATED TO YOU 5STAR ✨✨ ASSOCIATION*




5 star's ✨✨ online writer's association 👌




Part 27


Shi kuwa deeny gaban sa ne yaci gaba da faduwa wato kawun haleema kenan aka bawa dodo hawaye keta kwaranya a idaniyar deeny wai an kashe haleeman shi da kuma sis shi maryam da yake matukar ji da ita wato dai yana santa sosai a rayuwarsa  bayada babban gurinsa da ya wuce ya farantawa ummansa da kuma yar kanwarsa wato maryam tunda baban su baya raye kuma shine namiji haqin su na kansa wani xazzabi ne ya rufe deeny.


Maryam ce zaune kan wani gado na kara ta dafe kuma tu wato tayi tagumi tunanin ummanta kawai take wasu yan siriran hawaye ne suka kwaranyo haka haleema ma da take kwance kwakwalwarta sai juyawa take cike da tunani iri iri tama rasa wanne zatayi shin waye mai neman hallaka mu shin wanee hali deeny na ke ciki shin umma da abba ya xasu ji na rashina bayan basa san yi nesa dani ko kadan idanon ta cike  da kwalla ta tashi zaune ganin maryam a gefan gado ta zuba uban tagumi  maryam maryam inji haleema tunanin me kike. Tuni maryam ta dago tare da sa zane tana goge  hawayan fuskarta. Nan haleema ta fahimta cewa duk ashe daya ne halin da muke ciki... Ta dafa kafadar ta haba my sis ki saka dangana a zuciyar ki mn mu barwa allah komai shi zai  yi mn maganin wannan al'amari ba kuka ne abunyi ba... Aneesat ce ta shigo ganin su a wannan yanayi ta fahimta tunanin gida suke yi.duk da sun so su boye wa anne anma saida ta fahimta haba yan uwana nan fa kamar gidan ku ne ku kwantar da hankalin ku dama ynx daga wajan maman mu nake shawara muke yi yanda za'a maida ku gida ku kwantar da hankalin ku... Tabbas sunji dadi sosai da jin kalaman anney  gaba daya hmm sis anney kenan hb ba komai amma gsky muna so muga iyayan mu domin basu san ko wane muke ciki ba kinga in sun gammu hankalin su zai kwanta... Yaro ya shigo da salamar sa anney wai ana kiran maryam bata tsaya ko jin waye ba tace . je kace gata nan  domin anney tuni ta kyaro su wato tana lura da abunda ke faruwa tsakanin maryam da kuma isa. Ya zaki ce gani nan bayan baki san kowa ke sallama ba shin waima cikin gari  nan waya san ni da har zai aiko kuma wai ace maryam tazo ma..  Anne tayi murmushi ai sai kije ki gano mn ko wannan abun mamaki tare da nunawa alamun bata san ko waye ba cikin zolaya kanwar mu ah gaskiya kinzo kauyan nan a sa'a kinga shikenan sai mu barki anan. Suka sa dariya gaba daya. Inga ko waye tunda kun matsa  ta ce anney ara min hijab dinki gashi can a akwati na dauko. Ya mata daidai kuwa kamar dama nata ne..


A tsaye ta iske shi ya harde kafafu ya sai kara da ya rike a hannun hagu yana wasa da shi hannun daman kuma yasa shi cikin aljihun wando..

Assalamu alaiki ta fada wani irin sauti mai dadi yaji   a zuciya yace dama hk muryar yarinyar nan yake ashe..


Amin wa'alaiki salam warahmatul lahi taa'alah  wa barakatuhu:  sanda ya cika amsa salamar  cif  cif.


Gefe daya ta samu ta tsaya nesa da shi kadan  ita kam ta kasa dagowa da kanta  domin this 's first time  nata na tsayawa da wani da namiji ..



Maryam kenan sarkin kunya shin ko dai kema yar fullani ce kamar mu amma ai ke kunyar taki tayi yawa ma..

Murmushi kawai tayi domin ta gane yaya isah ne shi isa taki ma dago kanta domin tsoran abunda take ji in ta hada ido da shi wato faduwar gaba


☺ pls sis dago kanki ki kalle ni ya fada yayin da ya dan kara matsowa kadan kusa da ita.


A hankali ta dago kai  wow handsome dama haka wannan bawan allah yake da kyau ashe duk ganin da nake mai zaije farauta ne amma duk da haka yana da kyau saidai kayan da yasa sun karq fito da zallan kyawan sa wanda haka yasa ta kafe sa da ido shima dai abun ya daure mai kai ta tsaya sai kallan sa take...

Um dama so nake in gaya miki...  Kuma sai yayi shiru ka fada mana a zuciyarta ta fadi hakan gani ya kalle ta tayi saurin sunkuyar da kai ashe yaji abunda tace... 


Maryam ba wani abu bane dama ina so in gaya miki ina sanki ina kaunar ki tunanin ki ya hanani sukuni ko ina naje bana jindadi in ban ganki a gunba idan na rufe ido ke nake gani nayi tunanin cire hk a zuciyata sakama kwan ni dan kauye ne ke yar birni ce kinga kuwa auran mu bazai yuyu ba amma dai yanda sanki ya addabi raina yasa ni dole in gaya miki ko naji dan sauki...


Farin ciki ne ya ziyarci zuciyar ta hakika taji dadin kala man sa wannan ne na farko da namiji ya taba cewa yana santa abunda ko da wasa ba'a taba gaya mata ba kalmar so kenan yayin fadarta sai bakin ka ya fara bari duk jarumtakar ka bama kamar first time haka duk macen da aka furtawa a take a waje sai taji chanji lalai so halitar allah ne juyawa kawai tayi da niyar tafiya ita duk kunya ta dabai baye ta..


Maryam tsayawa tayi chik baki ban amsa ba zaki tafi pls ki taimaki zuciyata karta fashe mn... Juyowa tayi ta sakar mai tatausan murmushi mai dauke da sako saidai shi bai iya karanta iri  words din jikin murmushi ba  kawai cikin gida ta juya ta shige............. ..............



https://m.facebook.com/groups/1232550283531628

Bigboy isah ne♥♪













🔫.BANI NA KASHE TABA 😫🔫.



  Na big boy isah


.  *DEDICATED TO YOU 5STAR ✨✨ ASSOCIATION*

.


5 star's ✨✨ online writer's association 👌


.
Part 28


.

Cikin rashin gamsuwa isah ya koma gida yana ta tunane tunane shin me yarinyar nan ke nufi ai a so baa dole idan bata so na ba saita fada ba kawai a wuce gun isah ne shi kadan yana tafiya yana zancan zuci....


Maryam kuwa tana shiga dakin duk suka gyara zama wato haleema da anney wai sai ta fada musu waye yazo gunta fur taki fada sukayi sukayi anma tace kawai bata sanshi ba. Anney tace to ai nasan dole ya fada miki sunansa to ya sunansa ai nasan ko wane saurayi a duk fadin garin nan. Bai fadi min suna ba... Suka hau dariya wai bata da gaskiya hk dai suka ta zolayar maryam wacce ita kuwa tunani ne duk ya addabe ta..


Ina kwana umma lfy lau  aliyu a cewar mamar tasa sannan ya juya ga maman deeny suka gaisa.. Wai aliyu har ynz ba batun ko daya daga cikin su ne? Wllh mama babu wani lbr a cewar aliyu haka makarantar su maryam ma sun ce bata je ba ranar. Maman deeny ta yi shiru hawaye ne suka fara zarya a idanon ta a bun tausayi kanta ne ya fara sarawa da karfi dafe kanta tayi tana inalila hii  sakamakon kanta da taji yana juya da sauri juwa ta dauke ta luwww ta dauke wuta.. Da sauri sukayi kanta a kidime suka kwasa sai asbiti akayi Emergency da ita duk a gigice suke sun ma kasa zamq da kyar aka lalashe su da cewa jinin tane ya hau ynz tana bukatar hutu anjima zasu iya shiga domin ganin ta ....



Ban garan yazeed kuwa

.


Naman suka hau ci kallo daya xaka musu ka fahimci ba imane a tattare da su gaba daya yanda suke cin abinci da sasan dan adam a ciki amma su ko a kansu tsohon cikin su ne yace gaskiya badman man kayi mana asara kasan fa ogan mu wato dodan asirin su yafi bukatar jinin yan mata amma ka bari su mugu suka kashe su. Dad ba haka bane a duk cikin yaran ba wanda su mugu suka sama damar kubuta da su a inda suka iske su a nan suke sheqe su.. That gud. Kasan fa allah ne ya kawo mn dakwale har hudu police 3 da kuma wani 1 dan karamim cikin su.dad kace meat in police ne shi isa na gansa da baki baki. Lolz. Hahaha sukayi wata irin dariya tasu ta marar imani wacce suka saba when mugunta.  Tashe muje ka gansu inji tsohon nan. Ya kalli wasu dake tsaye kmr bayk  yacekuje ku kaiwa wadan can naman abinci mn ko so kuke sai sun rame sun zama kashi ne.






Su yazeed ne suka shiga dakin ajiya wato inda su deeny suke  kallan deeny yake kamar yasan shi saidai ya rasa a inane gaba daya kan yaZeed ya daure to shi a ina yasan wannan. Zuwa yayi gaban deeny ya tsuguna yana so ya  tuna wani abu amma ya kasa  kai kamar na sanka.. Denny kuwa kallan sa kawai yake. A ina. Inji deeny. Shiru kawai yazeed yayi dai2 lokacin ne aka shigo musu da abince plat uku ne aka bawa deeny daya suma sauran aka arajiye musu  nasu. Kamar jira suke  dama suka   fara aika abincin nan deeny ne ya yi kokarin da katar da su pls stop an eating this food. Ya fada wata irin harara dan sandan ya dakawa deeny almun ya kyale su dai deeny kuwa da ya karewa abincin kallo tsaff sai ya ga akwai nama mutum da sauri yasa kafa ya hankadar da abincin ya zube ..







Assalamu alaikimm. Suka amsa mai gaba ki daya yan majalisan. Zagayawa yayi bangaran abokin da wato salmanu ya zauna kan dan guntu  iccan da yake a xaune abokina waya tabo ka ne naga duk ka wani canja fuska ya tambayi isah. hmm abokina zo muja gefe ina san magana dakai salmanu ba gardama kuwa ya tashi suka koma gefe isah ya kwashe duk abunda ya faru tsakanin sa da maryam tun daga  A  haf Z yace to amma naga alamun yarinyar ba sona take ba jifa yanda na dame ka a kanta ko da yaushe tunani na gareta ne amma kaga fa abunda ta saka min da shi kenann.. dariya  salmanu ya kyakyace da ita hada su rike ciki.  bana san haka fa kai wato nazo na fadama damuwata wato abinda zaka min kenan ko kasan fa na tsani dariya isah ne ke fadan haka. Salmanu ya dafa kafadar sa yace Could down abokina nasan baka fahimta bane kawai amma a hakika nin gaskiya congratulate abokina domin i sure her accept ur.. Wanni irin dadi yaji baisan ma lokacin da ya rungume salmanu ba dan tsabar murna. Ur sure. Yes aboki domin kuwa murmushi ta shinr tabbacin hk sannan ba yanda xa'ayi in mace bata sanka ta maka murmushi a tym din da ka furta mata so saidai ma ta bata rai.  Yaya isah wai ance in kira ka. Wani yaro ne dan makwabtan su aka aiko. Wake kirana isah ya tnby yaran . abban ku .ok jeka ce gani nan zuwa . yauwa salmanu ina godiya da jin wannan gagarumin  albishir naka sannan ynz taya zan gane hk gsky ne idan naje gidan..

Kawai abunda zakayi shine ka mata murmushi in kuka hada ido sai kaga kalan martanin da zata dawo maka dashi inji salmanu. Nan sukayi bankwana. Isah ya nufi gidan nasu. 



Assalami alaikum3 ya maimaita amma shiru kake ji gidan kamar ba mutane. Saida ya zo wucewa upstairs sannan ya fahimci akwai mutum a armchair dake living room din wato parllo. Ta dora hannuwa biyu. Haba hajara miye haka me yasa zaki dorawa kanki damuwa da yawa  bayan haka allah ya kadarta haka yayi niya ya faru gare mu kisawa ranki dan gana mana.sai lokacin ma tayi farat ta dago alhj  ashe ka dawo tana goge hawayan da su. Haba maman deeny ynz dama duk wannan kugin da nake faman yi bakya jini hakika nin gaskiya ta bashi tausayi domin yanda take ji da yar tata rabuw da ita dole yasa ta cikin rudu. Rungumota yayi a jikinsa yana share mata hawaye kamar yarinya. Ita kuwa sai shesheka take tana cewa yanzu shikenan haleema na yanzu shikenan..  Ta kara kakame alhj tare da kuka mai tsuma rai shi kuwa yaci gaba da lalaban ta yana lalashin ta...




Maman deeny kuwa jiki yayi dama dama amina ce zaune kusa da ita kowa tayi shiru ba mai cewa uffan a cikin su. Lokacin ne sukaji an bude door din room din da suke ciki aliyu ya shigo dauke da....... ..  .






https://m.facebook.com/groups/1232550283531628

Bigboy isah ne♥♪










🔫.BANI NA KASHE TABA 😫🔫.



  Na big boy isah


.  *DEDICATED TO YOU 5STAR ✨✨ ASSOCIATION*

.


5 star's ✨✨ online writer's association 👌


.
Part 29







.

 Aliyu ne ya shigo dauke da ledoji guda biyu a hunnunsa. Ya ajiye ledojin  tare da dagowa yace mama ya jikin maman deeny. Da sauki ai Alhmdulilah saidai doctor yace ta rage tunani  cus. Duk shi yake kara zafin ciwan  .



Yaja nunfashi  tare da cewa to allah ya bada lafiya ga abinci nan ai sai ki bata ko kema ga naki ya mika mata ledojin sannan ya mike ya fita  maman deeny kuwa duk ta wani rame tana jin su duk abun da suke kuma idan ta a bude amma bata iya cewa komai ba...



Deeny kuwa tunanin tserewa yake domin kuwa yaji yazeed yace zai kawo baban sa. Yace a ransa ai gwara in fita ko ba komai da zan taimakawa kawun haleema kuma zan sake ganin ummina ko sau daya ne kafin a zartar da hukunci a kaina. Juyawa yayi ya kalli yan sandan nan yaga sai barci suke abunsu kamar dakin uwarsu  shi kam kwana 2 da yayi a gun ko gyan gyan di baiyi ba.. .



BAN GARAN ISAH KUWA..



shiga yayi dakin baban nasu da sallama abban nasa ya amsa. Bayan sun gaisa yace mai dama ba wani abu ne yasa nace a kiraka ba illah in fada maka maganar da mukayi  dazun muka tatauna da mahaifiyar ka a kan maganar yaran nan   kaga yau kwana 2 kenan bamu san wane hali iyayan su ke ciki ba ya kamata mu maida su ga iyayan su dan haka ina so zan baka kudi gobe da yamma ka kaisu gida domin suna cikin hayyacin su zasu ganne gida. Isah kuwa gaban sa ne ya fadi ji yake ai shikenan zai rasa maryam dinsa idan suka koma domin shi har ya sakan kance ma dan baiji ana mgnr koma war su ba. Dan hk sam shi baiji dadi ba da magnr abba.


To abba yace. Sannan yace baba kabar kudin ka ai ina da kudi zan sa ynz su shirya goben sai mu tafi.

To allah yamaka  albarka  yanxu tashi ka kira min mahaifiyar ka tare da su yaran.

To baba ya tashi ya nufi dakin umman nasu ya isar da sako sannan..


Ya nufi dakin anney su maryam da suke zaune sun gama cin abinci sai hirar duniya suke maryam ce aka bari a kwano sai sude kwano take  wai miyar tayi dadi wato taji daudawa lol.


Hmm ni wllh wani abu ke ban mamaki 


Anney tace  miye kuma wannan maryam.

Wai wannan baiwar allahr mn ta nuna haleema da yatsa cewa tayi fa bata cin tuwo miyar kuka in ba nama. Zumbur haleema ta tashi daga dan ringisawar da tayi kiji yarinya da sharri to waye ya gaya miki yaushe mukayi dake.


Kai haleema kiji tsoran allah kin manta ranar da kika zo gidan mu nace in zubo mn kika ce wai bakya ci. Ko dai ranar a koshe kike.


To ai ni ba wannan yake ban mamaki bama ji fa yanda kuka ware kuna cin tuwo amma fa ni gani nake ba dan allah kuke cin abincin garin  nan ba sai dan yunwa inji anney.


Gaba daya suka kwashe da dariya. Gaban maryam taji ya dan buga shi yasa ta sasauta dariya   5sc after sai suka ji sallama wannan ya sasu rage dariyar amma duk da haka a cikin dry suka amsa salama  isah ne ya shigo dakin ya tsaya yana kallan sarauniyar tasa so yake ta juyo ya aika mata da sako amma taki juyowa sai su anny ne suke gaishe shi...



Ya amsa itama sai daga baya ta gaishe sa ina wuni yaya isah a cewar maryam cikin wata sweet voice dinta. Su haleema ne suka hada ido alamun dai akwai wani abu kenan a kasa. Shima kam cikin wata sanyayar murya ya amsa mata tare da cewa sis anney an sama kawaye wato ba ko futa dandali ko.


Smile tayi tare da cewa my broz kamar ka sani kuwa domin ni har nama manta da fita zuwa dandali  zuwairah ma kaga taki biyo min ni kwana biyu ma bansan me na mata ba taki zuwa nan gidan...


Ai ke da ita baa san waye mai laifin ba domin kuwa ke ya kamata ki neme ta domin kinsan tallah take ko yanzu ma tana can ta fiddo tuwo tuwo a dandali...


Haleema tace wai me ake a dandalin dan allah yaya isah ka kaimu mu gano yayi murmushi.  Me kike ci na baka nq xuba bayan ga masu dandalin nan a kusa dake.


Ya nuna anney. Ya dan dafe kai  itafa wannan kawar taku bata mgn ne. Tana mgn mana wannan hmm uwar surutu kenan inji haleema  maybe kunyar ka take ji shi isa taki mgn. Maryam ce ta dakawa haleema uwar harara. 


Ah ai wllh gaskiya ta na fada kaji min yarinya. A cewar maryam.


Kinga kyale ta bari inzo ni kusa da ita in tmbye ta me ya hanata mgn. Zuwa yayi gab da maryan inds take zaune ya tsuguna.
Yace.................... King boy ne

Bi wannan line din domin join na grp dinmu

https://m.facebook.com/groups/1232550283531628













.BANI NA KASHE TABA 😫🔫.
        Part  30 & 31


  Na big boy isah


.  *DEDICATED TO YOU 5STAR ✨✨ ASSOCIATION*

.special thank 2 ur   sis maryam  kd. Queen ameena.  Sadeeya ak nasir  with fatima musa. .ina godiya a gare ku naji dadin addu'ar ku allah ya bar zumunci 😍


5 star's ✨✨ online writer's association 👌


.
Part 30






hjy maryam kenan laifin me nayi kuma da ba'a min magana. Idan laifi nayi ai gwara a fadan dan in gyara laifina ko.

Maryam dan kauda kai tayi gefe cike da kunya bakayi laifin komai ba bro..


Yauwa hb har naji zuciyata ta dan sama sukuni... 


Su halema da suke ta kallan su abun ya bawa Haleema sha'awa nan ta shiga tunanin deeny ta allah sarki.


Anney kuwa hannuwa tasa ta toshe baki ta bushe da dariya. Shima isah dagowa yayi cike da kunya yayin da ya tashi ya nufi kofa cike da kunya. Har zai fita  kuma sai ya waigo  ni har na manta ma wllh duk kun jani da  hira... Baba na kiran ku  ku duka.





. dukan su sun halara gaban abban su isah. Suka kwashi gaisuwa sannan ya dora da bayani. Ba wani abu bane yasa na kiraku sai dan in sheda muku cewa gobe zan hada  ku da isa ya maida ku gida domin bamu san ko wane hali iyayan ku suke ciki ba a yanzu Kunsan dai ku ba yara bane. Ya kalli inda su halleema suke yace fatan kundai ji abunda nace...



To baba yaushe zasu tafi kuma dan allah baba zan raka su inji anney.



No ai gobe da yamma zasu tafi dan haka kuje ku fara shiri ma tun yanzu sannan kuma ke aneesa badake za'aje ba.


Ayya dad dan allah ka barni inje sai mu dawo da yaya isah.


In banda abunki annisah ai ba yanda za'ayi ki bisu duk da dai kun shaku da juna amma ai sai ki bari wataran kyaje.

Hakika ita dai bata so haka ba domin bata jayaya da iyayan nata shi yasa taja bakin ta tayi shiru.


To mun gode abba ba abunda zamu iya cewa sai dai allah ya saka muku da alkhairi. To ameen ku tashi kuje sai da safe ko. Kai kuma isah goben ka shirya da wuri fa to abba.



Ku tashi ku tafi..


Yazeed ne yayi shiri tun da safee ya fito a shirye a dinner ya iske su abba yaje ya zauna bayan ya gaishe su. A nan yake fadawa  abba zai koma gida amma inaga kwana biyu zanyi. In dawo domin ko kaya bazan dauka ba. Abba yace to ai hikenan amma jiya ina kaje ne har na dawo ban iske kaba sai maman haleema ke gaya min kazo. Yadan sosai sosa kai eh wllh dad abokanaina ne suka tsare ni. Hmm yazeed kullum in kazo inamaka warning a kan bad friends ka kiyaye abokai marar sa tarbiya domin ba abu mai kyau bane. To dad ai abokan kasuwanci nane. Nace sis zeesa kasuwancin me. Tace na sheqe mutane mn lol.


Karfe 8;00 tuni sun kammala breakfast

8:30 yazeed ya daga


Deeny kuwa tunanin hanyar tsira yake  yace tabbas dole in bar gidan nan yau ko ta halin yaya. Hannu ya daga yana add'ua  ga yunwar da take cin sa domin shi kam yaki yarda yasha ko ruwan gidan.

Kamar kullum yauma haka  aka shigo karfe 9:00  aka kawowa su  deeny  breakfast  amma shi ko kallan abincin baiyi ba.


Mai kawo abincin ne yaje yake gayawa tsohon nan cewa yaran nan fa yaki yarda yaci abinci kuma a dokar wannan gidan sai wanda yaci abinci shine ba zai tsira ba. Ya juya ya kalli wani dake can tsaye kato ne duk jikin sa a murmurde baki ne wul wul da shi kamar gawaye bashi da riga shi isa na hango kirjin sa sai sheqi yake kmr an shafa mai. Kallo daya zakama katan nan ka tsorata domin indai ta bangaran girma da murdewa ne sadauki to lalai wannan gardin ya cika sadauki.
Ya kira shi da wani suna yace kaje  ga daya daga cikin yaran can yaki cin abinci kuma kasan cewa a tarihin nan gidan ba wanda ya taba shiga ya fita in ba yan kungiya ba. Maza kaje ka tsorata shi kuma banda duka ko ka tusa mai domin idan kayi hk ma a banza dole sai in mutum ne ya dauka abincin yaci da kansa tukun.  Ok sir kawai gardi said. Ya juya ya nufi dakin da su deeny ke ciki...






9:30   su anney ne ke wanke wanke suna tadi to mu da ake cewa mu shirya bayan ko kaya sai wanda suke na jikin mu.  Lah kaji min yarinya to da ace bamu wanke na jikin mu din jia ba to da fada min how. Inji maryam.  Ke ki kiyaye ni fa wllh na kusa change 2 ur aunt cus daga mu koma za'a dare mu nida brox in ki.  Tsaki taje tare da cewa to ke anney kinji fa wai so take ma ta tsere wato wai taje taga masoyin ta. Hmm kyale ta dai nasan irin zaman da zanyi dake wllh ta nuna halleema da hannun yauwq anne wai ke baki da saurayi ne a duk fadin garin nan ko dai babu mashin shinine. Hhhhh yar sa ido kawai. Inji haleem. Haleema kyale ta yau tsokala take ji ita da xata tayani miss kuma mgnr saurayi ke dai tunda kin sama naki kin zo kin dauke smart din garin ba shikenan ba. Wata kalan harara ta dakawa anney waye?  Hmm kedai kika sani. Lokacin da suke tattara kayan wanke wanke. Yauwa sisters dan allah ku taimaka min ku lalabi abba mybe in kune zaiyi hkr ya barni in biku tunda dai yau yaya isah zai dawo. To eh mun yarda amma sai kin zagaya damu wannan rigar taku tinda kinga har ynz bamuyi yawo da rana ba. Au dan wannan ne ai ba matsala bane yanzu dai kuyi wanka tukun na.  To ke fa yaushe zaki yi wankan. Tabb to ni da ba dani za'a ba wankan me zanyi aradu banayi ba.


Dariya suka hau yi kamar me... Mama Wai annest bazatayi wanka ba sai za'a je anguwa. Maryam ce ke fadi wa maman


Part 31


Hmm ai kadan ma kuka gani ko dandali idan zata kwaskwarima kawai take sai uban jan baki da take laftawa wai amma a hk har samari ke bibiyar ta. Hhh to inna amma naga tunda muka zo ba wanda ke zuwa ai ni har nama farq tunani ko ba mashin shinine.

Hmm ai in gaya miki  abun nan ahn ahn  maryam kike toh wllh duk wanda yaxo korar shi take wai ita dan mai gari take so. Maryam tasa hannuwa biyu ta matse dariyar da ta taho. Ai kuwa inna.bari in taya ki gyaran dakin nan inje inta tsokalan ta.ah ah maryam da kin bari  ku yan birni ai wannan ba aikin ku bane. Maryam tayi murmushi lokacin da take shinfida  bedsheets lah mama kenan to wllh wasu yan birnin ma aikin da suke in kika gani sai kin rike baki...aa maryqm ai bazaki hada ba da nan da can kinga mu fa nan ko dakan fura aka barki da shi ya isheki  balle ke zaki jawo ruwa kuma ki zo kiyi girki kuma fa wani lokacin ke xaki surfa ki kuma daka ..


Gabanta taji ya dan fadi lokacin da ta tuno da dan guntun san isah dake makale a zuciyarta to shi wannan dan mutumin idan ya aure ni a nufin shi ina xai ajiye ni to al qur'an nidai bazan zauna a kauyan nan ba wannan uban aiki   .

To  dama jan ruwa zanji ko dakan ko girki. Wai fa nan ma ba su kadai bane aiki wuni. Mama ce ta katseta daga thinking din da ta ke yi..


Umman anney din ta danyi murmushi ko dai abubuwan ne nan uku kadai dana lissafa sune har suka saki dogon tunani . ta dan zaro ido mama bayan wannan harda wasu ayyukan kuma.  Sosaima ai wannan wai wanda suka xama dole ne kawai na fada miki amma ai akwai saura da yawa ma ko in lissafo miki .   aa barshi wllh mama karki dada tsorata ni wllh. Ai sai ynz ma na fahimci  matan birni  hutu kawai suke kinga ba kowa take girki da ice ba  wasu cookrgas ma suke aiki da shi...amma a hk ma sai shegen korafi. Kuma kinga ruwa mai gida ke saya haka ma idan kina san fura shi xai sayo.


Mama tace kwarai kuwa kinsan fa muma munyi zama a cam  kusan shekarar 9 a can..

Lah allah mama kuma me ya dawo daku wannan kauyan..


Mamar tayi shiru kadan sannan tace kai maryam gaskiya fa yau kina ji da surutu. Dama hk kike ashe. Maryam ta dan rufe ido wai alamun kunya mama kenan.


Nine nace sis nasmat wllh ina san sanin abunda ya koro su umman anney kauye?


Sis nasmat tace hmm kishine kawai fa wai daga abba na niyan aure lol.

1:00
Yanzu

 An sallamo maman deeny Likita ya rubuta musu magun guna sannan yace musu su kiyaye kuma a guji abunda zai batawa ita rai ko kankani ne. Ya sallame su suka koma gida gidan kawu kenan gidan su aliyu.




Yanzu karfe  2:00



Yazeed ya isa garin abuja ya tsaya hanya ya danyi sayaya tsara ba kenan sannan ya karasa gida. Yana shiga su siyama sukayo kansa. Wato kanan sa ne su biyun dake sun san duk zuwan da zaiyi sai ya kawo musu tsaraba saida ya bawa kowa nashi tukun ya karasa ya gaida mum dinshi. Take tambaya lfy yace wllh lafiya kalau kawai na dawo yin wani abune ina dad. Bai dawo ba inji  hjt saratu wato mamansa kenan. Ok ya fada sannan ya tashi ya nufi up stairs...




Su maman anney kuwa da maryam suna daki sai hira suke abunsu lokacin sallah har yayi. Maryam ta fito  ta tarar da su anney har sun kusa kamala girki wato abincin rana. To uwar surutu kin gaji ko  ai muna jin surutun ki har nan halerma ce ta fada.  Cuno baki tayi tace anyi din yar sa eyes kawai. Zanyi maganin ki ai yarinyar nan wato ina aunty ki amma kike fadan wannan mgnr ko dan baki da kunya.  Eh din anyi ta harare ta sannan ta juya ga anne budurwr dan mai gari in gaisuwa fa idan yaxo hira yau a mika min gaisuwata. Anney kuwa daga jin hk ta gane mama ce ta fadi mt Tashi tayi ta bita da gudu da kara a hunnu suka hau xagaya gida. Sallamar da sukaji ita ce ta tsaida su..............King boy ne

Bi wannan line din domin join na grp dinmu

https://m.facebook.com/groups/1232550283531628







🔫.BANI NA KASHE TABA 😫🔫.



  Na big boy isah


.  *DEDICATED TO YOU 5STAR ✨✨ ASSOCIATION*

.


5 star's ✨✨ online writer's association 👌


.
Part 32


My friends i need u duha'a mura ta shake ni ku mun addu'a  allah ya rabamu da ita domin bansan me nai mata ba lolz.


.
Abban su anney ne ya shigo shine yasa su tsayawa cik daga inda suke suka daina guje gujen.  Abba ina wuni kmr hadin baki duka suka fada ya amsa lfy lau sannan ya kalli anney ke me yasa bakya ji ne kingani ko ai shi yasa nama hana ki ki bi su dan karki je ki kama yi musu rashin jin a can..



Kwalla ce ta cika mata idano aa wlh abba xan natsu wllh abba.

Abba dan allah ka barta mu tafi tare.Inji haleema kafin yayi magana maryam ma tace abba dan allah ka barta ta bimu tunda yau yaya isahn zai dawo sai su dawo tare. Jin hakan abba yadanyi jin kadan sannan yace to shikenan ba komai xata iya rakaku.


Wani kalan murna da farin ciki ne ya ziyarci zuciyan anney bata san lokacin da ta daka tsalle ta kamkame maryam tana dariyar farin ciki da shewa.   

Au kun gani ko kunga abunda nake gaya muku. Ayya abba farin ciki ne fa.anney ta natsu.

Wai ina yayan naku ne. wllh har ynz dai bai shigo ba abba. Ynz fa 1:30  kunga kuyi sauri ku shirya sannan kuyi sallah sai ku tafe can domin kuyi bankwana da gwaggo to abba..




Bangaran deeny kuwa..

Katan yana shiga deeny yaji gaban sa na faduwa gadan gadan kuwa ya nufi inda deeny ke zau ne  tray din abinci katan ya dire a gaban deeny ko mgn baiyi wa deeny ba kawai ya bata rai yana hararan deeny da jajayan idanonsa. Ganin deeny ya dake ko dan firgita baiyi ba yasa katan nan ya kara turo abinci gaban sa. Ci dan ubanka.da wata basamudiyar murya yayi mgnr wacce  idan . nasmat ce akawa sai tayi zawo lol.nan deeny ya fara tunanin wanne abu tabbas akwai lauje cikin nadi to su miye damuwar su dan naki cin abinci to wllh bazan ci ba. Hk ya fada a zuciyar sa. Bazan ci ba.hk kawai ya furta. Katan kuwa ya fusata ai nin wata kalan tsawa ya dakawa deeny wace saida tasa duka parllon ya rude sauran police din kuwa su biyu kan kame juna sukayi hade da sa hannu suka toshe kunnuwa domin karan bana wasa bane. Deeny kuwa ko kallan sa baiyi ba saidai kawai rufe kunnan da yayi..


Kai wllh badan ance kar in dake kaba da yau saika dandana axabar da baka taba ji ba a rayuwar ka dan iska kawai wato kai har wani jiji dakai zakawa mutane ko  oya zanje in dawo kuma wllh ka tabbatar ka cinye abincn nan ya ya bude door in daki ya fita shi kuwa deeny kallan sa kawai yayi yace ai kuwa zaka zo ka dauke abunka yanda ka barshi domin ni azumi nake ma .




Su anney tuni an shirya jin ance za'a da ita yasa ta yin wanka nan taje ta fara make up  duk da ta zauna a birni amma hk baisa ta daina haukan kwaliya ba Ta dan iya kwaliya hk ta zo ta lafta uwar Powder ja aka zo aka kara da wani janbaki shima ja ga uban eyes shadow an maka kai abundai abun dariya.maryam na shigowa ta kwashe da wata mahaukaciyan dariya sannan ta shiga kiran  haleema wai ta zo ta gani su anney anyi kwalliya dariya take sosai. Ita kuwa anney murguda mata baki ta shiga yi ina ruwanki yar sa eyes kawai lokacin ne haleema ta shigo dakin itama dai abun ya bata dariya amma  kawai  sai ta basar taje ta ce sis anney kyale waccan yar adawa ce. Nan haleema ta dan gyagyara mata. Wow masha'allah maryam ce ta fadi hk da tayi tozali da fuskar anney kinga yanda kikayi kyau kuwa annesah  ai yanzu ne kike annesah amma da anney. Sukayi dariya. Hk suka fito suka hau zagaya gari ko ina sai kallan su ake can suka hango wani saurayi ya nufo  su. Nan take anney ta wani daure fuska gabaki daya ta chanza fuska.

Maryam ta fahimci hkn to amma ta rasa dalilin da yasa anney bata rai hk. Sun danyi gaba maryam ta dawo baya inda taga wani saurayi wanda zaikai  15 years hk take tambayarsa wancan waye ta nuna saurayin da anney ta gani ta bata rai. Dan mai gari ne mn sunan sa ado. Kai amma naji dadi wllh amma kaci sa'a bani da ko kwandala amma da sai nama kyauta. Ta bisu a guje. Tana kai ku tsayani mn duk haukan anney yau dai kam ta sarawa maryam domin abunda take yi yau yafi karfin anney ma.



Isah ne a labe ashe yana kalan maryam yana binsu a baya duk abun da take yana gani duk sai yaji ta kara shiga rayuwarsa yaji santa ya kara shiga zuciyarsa da sauri ya bisu domin shi a yanzu ji yake baya so ya rabu da ita daidai da 1 second.............  Yo ai hikenan   good morning oll my fans


King boy ne

Bi wannan line din domin join na grp dinmu

https://m.facebook.com/groups/1232550283531628















🔫.BANI NA KASHE TABA 😫🔫.



  Na big boy isah


.  *THIS PG DEDICATION  TO YOU  AISHATU S MAKWAYO NINGi  RUKKAYA ALHAJI MARYAM SHEHU AISHA HAYATUDEEN WITH MY LOVELY SIS MARYAM KD LOVE U OLL THANKS 4 UR PRAYER TO ME*

.


5 star's ✨✨ online writer's association 👌


.
Part 33







Gida ya bisu saida suka shiga sun dan jima sannan ya bi bayan su. Maryam ce sai zuba uban surutu take domin yau yan hk ne a kan nata.

Salama sukaji anyi..

Salamar da tasa maryam yin shiru a dole isah ne ya shigo can nesa da su kadan ya sama wani tsohon tirmi ya zauna sanye yake da white t-shirt mai kyau ta kama jikinsa sai wando black jean ya gyara sumar kansa tayi luf luf duk da yake shi ko aski ba a kauyan nan ake mai ba yasha gyaran fuska abundai gwanin sha'awa. To ai sai ku gama bankwanan ko ma tafi ya duba agogon dake makale a hannunsa

Oh kunga fa ynx 3:30 to wllh 10mit na baku.

Maryam da take uban surutu daga shigowar sa taja baki tayi tsit daga eh sai aa kawai take iya cewa ita gaba daya kunyarsa take ji. Kowa ya fahimci hk amma duk sai suka kyale.


Isah ne daga can yace haleema wai ni kam me nawa maryam ne kinga daga shigowata taja baki tayi shiru bayan tun daga waje nake jin sautin ta...

Anney tayi farat Kunyarka take ji..

Ya harare ta ke kuma ina tuwanki . ah su sis annisa anyi wanka ina za'aje ne.


Yo ai dane za'aje baba bai gayama ba ta wangale baki.
Nifa ince kwaliyar nan ba'a banza ba inji kaka..

Haleema ce tace kai gaskiya anney an canfa ki da yawa wllh ke kowa yasan bakya wanka.

Kuwa ya kama mata dariya ita kuwa ta wani sha kunu..


Maryam dai kadan2 take satar kallan ya isah.

Shima din kallan ta yake daga sun hada ido kuwa sai ya sakar mata wani murmushi wanda ke karya mata hantar zuciya.

Nan dai sukayi bankwana da kaka ta kawo uwar tsaraba irin tasu ta kauye ta basu sukayi godiya da maryam har tace a barshi ya isah ne yayi mgn shine yasa tayi shiru.


Hk suka koma gidan su anney can ma aka yo musu tsaraba irin ta kauye har makwabtan su duk sun kawo kayan alheri  kunsan dai tsarabar  kauye  bata wuce irin kayayakin gona

Su gyada soyaya  yakuwa su goriba taura magarya.  Ai kuwa duk da yaya isah na kallam maryam hkn bai hnata cin goriba ba saidai tanayi tana boye fuska.

Su haleema Sunyi mamaki matuka ganin irin karar da yan kauyan nan suka yi musu gaskiya ko nan sunyi abunda yan birnin ma baza suyi ba.. tafiya suke sun nufi hanyar da zata kaisu wajan hawa mota.  Maryam a can gefan take gefan dama. Ya isa kuwa yana gefan hagu amma saida yayi dabarar da ya koma can gefan da take. Yau kam Alhmdulilah sun danyi hira da ita saida ya kasan ce su anney da halima suna hirar su dabam itama maryam da ya isah hirar su da ban yaji dadi kwarai ynd ta sakar mai fuska yau. Sun dan yi tafiya mai nisa tukwanan suka isa wajan hawa motar...... Karfe 4:00 daidai suka shiga. Motar kano. Dake dan kauyen nasu ba mutane saida suka danyi jira akayi lodi tukwanan...



Bangaran deeny..


Deeny fa ya fara jin maza domin ji yake kamar diyan hanjin sa zasu fado dan yunwa tsabar yunwar da yake ji tasa ya fara sallama rayuwarsa ma..



Abuja kuwa..

Yana zaune shida yan kannansa a parllo suna kallo shi kuwa yana tunanin ya zaiyi yaja dady gobe zuwa kano kuma inma sunje ya zaiyi domin ya kaishi gidan tsafi tunda ya riga yayi kyauta da shi. Salamar abba ce ta dawo da shi daga tunanin da yake yi. Cikin fara'a ya tashi ya tarya abban.


Hjy saratu tazo ta karba jakar hannun alhj wato baban sh yaxeed  shi kuwa hannun yaran nan shi ya kamo suka zo suka xauna yazeed ya durkusa ya kwashi gaisuwa. Sannan ya tashi ya koma kan kujera.

Kai kuwa yazeed me ya dawo dakai wannan karan kai da kake yin kwana2 or 3 wllh dad na manta wani abu ne amma gobr zan koma kuma sannan ina so goben in ba damuwa mu tafi tare domin mai gidan mu yace yana san ganin ka..

To masha'allahu nayi murna sosai kuma naji dadi domin kuwq na dade ina san in san aikin ka wato dayan busines din da kake kaga kuwa gobe ko inada aiki dole in barsa mu tafi tare tunda ba dadewa zqmuyi ba ai har momyn ka zamu iya tafiya da ita ya kalli hjj saratu yace ku shirya gobe zamu tafi kano domin kuwa kinga batan halleema yau kusan 6 days bamu je ba kullum sai faman waya. To allhj allah ya kaimu kawai tace shi kuwa yazeed wani irin farin ciki ne ya lulube zuciyar sa domin kuwq ya sama hanya mafi sauki da zai ja abban shi gidan sheqewa............

Karfe 7 su maryan suka iso garin kano Alhmdulilah sun zo lafiya.. ............ Ni kuma nace bani da lfy ba yo ai hikenan

Naku big boy pls prayer 4 me my friends wllh mura ta shake ni da yawa https://m.facebook.com/groups/1232550283531628












🔫.BANI NA KASHE TABA 😫🔫.



  Na big boy isah


.  *THIS PG DEDICAT TO YOU MY SISTER ANEESAHT
.


5 star's ✨✨ online writer's association 👌


.
Part 34




A tashar mota suka sauka. A daidaita suka hai basu zame ko ina ba sai kofar gidan su deeny. Wani irin farin ciki ne da azarbabi ke azalzalar haleema tun kafin su sauko da zata ruga cikin gidan yau fa 6 days rabona da gidan nan. Mai zuwa sukayi suka kwankwasa gidan daga ciki mai gadin ke tambaya waye.  Haleema tace nice..


Sautin haleema ne ya daki dodan kunnan sa amma shi ya karyata hk domin shine yaga gawar haleema wata zuciyar tace mai haleema ce wata kuma tace mai wannan mai kalan muryar tace. Kara bubugawan da akayi ne ya dawo dashi daga tunanin da yake. Su anney kuwa ana tsatsaye sai waige waige take domin anguwar masu kudi ne komai a tsare yake a anguwar..

Dan bude wa yayi a hankali. Ganin haleema a tsaye tana kallan sa yasa yin sauri ya tura kyauran ya rufe da gudu ya nufi cikin gida yana kiran fatalwa2 su ahj sanusi ne da kuma maman haleema a parllo ya kunna kallo wai dan ya dan kore musu kewa amma ina ai duk lokacin da ta tuno yar tata sai ta fara zubar hawaye alhj ya hau lalashi..


Adamu mai gadi ne ya shigo a sukwane domin masifar gudun da yake abun ya baci da kyar da alhj ya daka mai tsawa ya hadawa kansa birki..


Kana da hankali kuwa adamu ya zaka shigo mana gida hk da gudu kuma ko sallama babu.

Wllh alhj abun ne ya tsorata ne alhj fatalwa na gani yau kiri kiri da ido na alhj.


Kai bana san shirman banza a ina kaga fatalwar.

Alhj wllh wllh karku je fatalwa ce tayi shigar yar ku haleema ta zo gidan nan domin ni nasan ba haleema bace haleema tuni ta mutu...

Jin an anbaci haleema jikin maman haleema ya dau rawa duk ta kidime tana ina muje ka kaimu tana fada cikin wata murya mai gargada.

Alhj wllh karku je.... Yi mn shiru matsoraci kawai sai yau nayi ladamar daukar ka aiki ita kuwa maman hallema tuni ta fita waje ta nufi gun gate..


Shiru shirun da sukaji ne yasa gaba daya maryam ta kosa taga mahaifiyar ta dole ta takura musu da ita fa tafiya xatayi in yaso da safe zata zo. Ya isah kuwa da jin hk yace to ynz yanda za'ayi su su tsaya a nan kafin azo a bude mu muje gidan naku. Hk aka bar anney da haleema a gun. su kuwa suka tafi gidan su maryam dake anguwar ba nesa.  A tsakanin su. Tafiya suke suna hira ya isah ne keta jadada soyayyar sa a gareta ita kuwa ba abun da take so a yanzu da ya wuce taga mahaifiyar ta. Tun daga nesa ta hango gidan a rufe alamu dai ba kowa kenan.basu tabbatar da hakan ba saida suka karasa suka iske gidan a garkame da kwado. To ina mum ta tafi kuma ma ai ya kamata mu iske ya deeny a gida domin a gida yake yin sallahr maghriba. Shidai isah ya tsareta da kallo sauraran zazakar muryar ta yake ji yake kamar karta daina domin kuwa bazai gaji da  jin muryarta ba.



Kallan shi tayi duk da dare ne hkn bai hanata gane ita kawai yake kallo  ba dake akwai fitulu a layin nasu. Murmushi tayi ya isah wannan wane irin kallo ne hk kamar baka taba gani naba sai yanzu. A kunyace yace ina wani tunanine maryam idan na rasaki a matsayin mata bansan wane hali zan tsinta kaina a ciki ba bama wannan ba. Abunda yake kara bani tsoro shine ni fa dan kauye ne kuma a halin ynz ma bansan ya matsayina yake a gunki ba..


Hakika zantukan sa sun sata jin tausayin sa. Ya isah kasani cewa tun haduwar mu ta farko dakai na gane cewa kaine mijin da zan aura badan komai ba ma ko dan faduwar gaban da naji a lokacin. Ya isah duk abunda ake nema a jikin namiji ka mallakr sa sannan duk macan da ta same ka ta wuce gori tabbas ina sanka har cikin zuciyata ba wanda ya isah ya rabani da kai ya isah kai kadai ne kuma namijin da ya fara furta kalmar so a gare ni ba shakka ina sanka in kuma kaunarka.


Wanni farinci ki ne da baya musaltuwa ya ziyarci zuciyar ya isah bai san lokacin da hawayan farin ciki ba daga idanon sa. Sun dade a tsaye sunawa juna kallan kauna sun kafe juna da idanu. Sai can maryam tace yaya isah muje gidan kawu nasan maman mu baya wuce tana can. Murmushi yayi tare da cewa to muje. Ko...



Da sauri tazo ta kama gate tana kakar2 tun bude wa. Alhj ne ya karaso waje hb safiya ya zaki zo ki dinga kokarin bude mana gida bayan baki san ki waye ba kisawa zuciyarki natsuwa mana.  Suna cikin haka ne sukaji an kara buga gidan tare da cewa ado ka bude mn nice haleema ce fa.  Jin muryarta ne ya kara rikita gaba daya iyayan nata sai ya zama ana rige rigen bude kofar ma. Suna budewa haleema ce alhj wllh ita ce ko dai  gizau take wa idanona hjy ce ke fadan hk lokacin da take nunawa alhj sanusi. Abun tausayi yanda hjy safiya ta kidime da ganin yar tata halerma itama kukan farin ciki ta fara da sauri ta zo ta rungume maman nata tasa kanta cikin jikinta tana kuka tana cewa mama nice fa. Ta kasa cewa komai kuka kawai take. Aneesah dake gun ita kanta saida tayi kwalla shima alhj hk......nima hk ku kuwa fa?

Yo ai hikenan bigboy ne ku tarye ni da anjima ♥ luv u oll my fans

https://m.facebook.com/groups/1232550283531628














🔫.BANI NA KASHE TABA 😫🔫.



  Na big boy isah


.  *THIS PG DEDICATION TO YOU MY SISTER ANEESAHT
.


5 star's ✨✨ online writer's association 👌


.
Part 35






Haka suka shiga gida rungume da juna sai kukan farin ciki suke yar da aka fidda rai da ita gashi ta dawo murna ai yau a gurin su hjy safiya bata faduwa hk shima alhj. Anney dai bayan su tabi kawai wanda su basu tambaya ko wacece ba hk itama bata fada musu ba...




Direct su maryam gidan su kawu suka nufa ita kam maryam duk da dai tana cikin zullumin ganin ummanta hk baisa ta share isah ba hk suke tafiya a jire sai fira suke irin ta masoya kamar dai wanda dama can sun shaku da juna. Sunzo wuce wa ta wajan wani mai lemu ne isah yace bari a sayawa umman mu tsaraba ko. Uhmm kawai tace. Lemun 300 ya saya aka zuba a leda sai kuma na hannun shi wanda yake sha yayi2 ta karfa tasha amma ina kunya ta hanata karfa. Basu dade suna tafiya ba suka karaso layin su kawu.


Maman deeny yau jiki yayi sauki zaune take a kan tabarma a tsakar gida ita dai yau ta rasa me yasa gaban ta ke faduwa time 2 time hk dai ta wuni yau tun tana tsammanin wani abu yanzu har ta daina ta kammala sallar isha'i  tayi addu'o'i ynz maman aliyu ce take jira domin suci abinci karya huce.

Su maryam sun karaso kofar gida shi isa yace bari in tsaya ki shiga idan kin sanar da su sai in shigo ko. Tace ok dear. Hakika yaji dadin sunan domin da ta shige saida yayi dan tsalle dan murna.


Assalamu"alaikum;  karima wato maman deeny kafe mai sallamar tayi da ido lokacin da take kokari tashi. Itama maryam daga inda take ta tsaya cik tana hawaye dan farin ciki. Haka dai sukayi cirko cirko kowa sai sharar hawaye yake. Ita dai maman deeny bata gaskata abunda idanuwanta ke nuna mata ba. Shi yasa ma bata karasa gun maryam ba. Suna cikin haka ne amina ta fito a dakin lokacin da ta gama prayer. Daga inda take ta tsaya. Hade da cewa wa zqn gani hk maryan kece kuwa. Lokacin ne ma maman deeny ta fahimci idanuwanta ba karya suke mata ba. Mama aminq nice. Hb a lokaci guda maman deeny ta taho da sauri2 gudu2 tayi hug in maryam tare da fashewa da wani kuka mai tsuma zuciya tana fadin maryam ashe kina raye maryam ina kika tafi kika barni cikin kuka take mgnr.. Itama maryam kuka take yi mai tsanani tare da farin ciki. Amina ma zuwa tayi ta rungume su hk suka kankame juna ba abunda suke sai kukan farin ciki..


Isah dake kofar gida a tsaye tuni shi yafara gajiya da tsayuwa ba abunda yake ji sai sautin kuka ciki2 dake tashi a gidan. Shi yasa ya yanke shawarar cewa idan yaga  yaro ya aika shi ya kirawo maryam..

Ana cikin hk sai ga aliyu da ya dawo daga wajan friends dinsa ya iske mutum a kofar gida yama isah sallama  sannan ya mika mar hannu  suka gaisa har aliyu ya juya zai shiga gida sai isah yace yauwa dan allah brox idan ka shiga kace anawa maryam mgn. Cikin rashin fahimta yace wace maryam kuma ai mu bamu da maryam a gidan nan. Eh ba  yar nan gidan bace ai zuwa tayi. Bai ce mai komai ba yasa kai ya shiga cikin gidan.yayi sallama yaji shiru sai sautin kuka ciki2 Ganin halin da suke ciki ne yasa shi karasawa da sauri maryam Alhmdulilah ya fada. Bari in shigo da bakon ya kika bar shi a waje. Lokacin ne ya fita ya shigo da shi..



Haleema kuwa sun gama koke koken su taja halleema ta nufi dakin su tace bari in shiga inyi wanka tukun. Sis anney ta amsa to halima gani tayi anney ta tsaya a tsaye sai kalle2 take ji dallah kamar wata baffalata na ki zauna mana. Hmm abun hada ba'a ko haleema. Nan dai tayi dariya ta fada toilet din. Anney kuwa kama baki tayib tace  ah   wai dama halima cikin wannan dollars din take amma har ta iya rayuwa a gidan mu wai hada cin abinci. Hmm gaskiya na jinjina miki. Tashi tayi taje gaban mirror tana kallan kayan make-up kala2 tym din halima ta fito daure da towel.anney Ta kalli hallima nifa wllh mamaki kiki kara bani wai dan allah ya kika ji dan zaman gidan mu da kikayi. Haleema tayi murmushi tace to ke me nufin ki ai ni dan banbanci kadane na gani. Hmm kadan fa kika ce? Nan dai sukai tayi. Da suka gaji da surutun sune anney ta shiga toilet itama domin yin wanka.


BANGARAN DEENY KUWA:


Karfe  11:00 PM

masifar yunwa da yake ji tayi over hk yasa shi tashi ya duba ko 'ina na dakin da suke amma baiga komai ba domin a wannan halin ko abincin gidan nan ma ya samu ci zaiyi. Kamar ance yaje ya taba kofa. Ya nufi kofar kmr wasa yana murdawa ta bude kuwa. Lekowa yayi ya duba ko 'ina baiga kowa ba. Ya juya ya kalli abokan nasa wato yan sandan nan sunci abinci sun koshi sai barci suke hada minsharin su. A hankali cikin sando ya karasa open din door in ya fito kamar ba kasa yake takawa ba dan sando shine har parllo yana yi yana waige waige. Wajan makeken kofar fita ya nufa zuwa yayi ya kama kofar da niyar budewa bisa mamaki sai ji yayi.......................sis abullee ta kore ni .lolz

good night to oll my fans


King boy ne

Bi wannan line din domin join na grp dinmu

https://m.facebook.com/groups/1232550283531628













🔫.BANI NA KASHE TABA 😫🔫.



  Na big boy isah


.  *DEDICATED TO YOU SARAKUWA TA ama alhj kabir  allah ya barku tare da mijin ki sannan allah yasa ya kara mik.........*

.


5 star's ✨✨ online writer's association 👌


.
Part 36



KUYI HKR FA YAU BAN SAMA DAMAR POST DA SAFE BA  BECAUSE OF BUSY




Wata mahauka ciyan dariya yaji an barke da ita "hahahaha" can kuma ya hahanga bai hange komai a gurin ba hkn ta kara basa damar sake kama kofan da niyan open inta. Amma kmr dazu dariyar kartai kawai yaji ya juyo kuma baiga komai ba. Hkn ya basa damar budewa duda yaji dariyan amma yasa hannu biyu iya du karhin sa ya ja kofar. Ai kuwa ta bude. Waige2 ya dinga a tsakiyan wannan makeken gidan baiga komai ba. Da gudu ya karasa gate in gidan su dama wai a ka idar wannan gidan sai wanda yaci abinci ne bazai taba  tserewa a gidan ba kuma basa kulle kofa domin tarkon ne su a gunsu barin gidan a bude. Irin dai darkon da su deeny suka fada. 


Yana fitowa daga gidan yayi wata hamdala Alhmdulilah'"  ya juya ya kalli gidan ya waiga ko i'na amma baiga koda alamun gida ba' yunwa yake ji matuka. Hk ya rinka tafiya jiri na daukan sa. Domin yau kwanan sa 3 baisa komai a bakinsa ba. Barks ya ringa ji a bayan sa. Sai matsowa suke. Ai kuwa kafin kace me. Washi nada2 karnuka ya hango sai haushi suke sun nufo shi. Gasu bakike. Ai kuwa yace kafa me naci ban baki ba" take yaji wani saban karfi a tare da shi tuni yaji yunwar ta bace wani masi fafan  gudu suke yi.....




Bayan gari ya washe

Tun 5:00 su alhj bashir suka dau way dake alhj sanusi ya fada musu tun yesterday cewa halima ta dawo. Shi yasa shike ta zumudi domin su zo taya dan uwan nasa murna.

Ban garan su halima kuwa tun a daran ta shaidawa su abban nata cewa tare da yayan anney suke su sun wuce gidan su maryam ne shine ya tsince ta. Sunji dadi matuka hk dai suka cewa yar tasu taje ta huta domin tana bukatar hutu ita kuwa duk ta damu tunanin  deeny take kuma har ynz ta tambaye su yafi a irga amna basu bata lafiyayan answer ba domin suma basa da amsar .

Haka shima bangaran su maryam

Aliyu kam kamar can dama abokai ne shida isah domin night din jia ma a gado daya suka kwana. Maman deeny tayi farin ciki sosai sai dai kuma in ta tuna har now batasan inda deeny ta yake ba. Sai kuma taji bakin ciki a can under her heart. Maryam tun da suka dan natsu take ask ina brox inta wato deeny. Amina ce ta kwantar mata da hnkli tace ta bari ba ynz ba tukun sai gobe sayi mgn.



Tun safe kafin su karya alhj sanusi ya aiko da mota yace yana bukatar ganin kowa da kowa na nan gidan kawu. Kawun deeny da yace a bari suyi breakfast mn . amma dan aike alhj sanusi yace.  Yace A gaya muku ya tanadar muku abun breakfast a can. Hk driver ya tsaya ya jira su suka dan kin2 tsa tukwanan suka tafi.

Ba'a bar kowa a gidan kawu ba.


A parllo aka hadu gaba daya aka shin fida tabarma a sanan carpet in kayan breakfast ne kala2 gasu nan an jejera da sai abunda mutum yake san yace a zazaune suke suna jiran su maman deeny. Cikin  30 second sai  gasu sun iso ko wane cike da farin ciki fall a zuciyan sa. haleema kam sai dubawa take amma bataga gwanin nata ba. Wato deeny. Hk suka je aka jejeru kawu da alhj sanusi saiti daya suke. Hk maman deeny da maman hleema da amina maman aliyu suma gefan su daya a kan carpet suke a zaune a hk suma su haleema grp dinsu daban suma su isah hk sun daiyi abun sha'awa kamar dama family ne dama duk anyi gaishe2 . Alhj sanusi ne ya fara mgn: to yan assalamu alaikum. Kowa ya amsa. Yace to a gaskiya baxan iya bayana muku farin cikin da nake ciki ba a yanzu. Sakamakon wannan al'amari mai ban al'ajabi da ya faru  wato batun mutuwar haleema. To a hakikanin gaskiya wannan jaraba wace daga allah sannan idan......


Wayarsa ce tayi ringing ya fiddo da fara'ar sa ya daga ganin wanda ke kiran nasa. Wato yayan sane alhj bashir da suka taho daga abuja. Yace gasu nan sun karaso cikin kano motar su ce ta dan sama matsala a turo driver ya dauko su. Cikin farin ciki. Abba yace to shikenan yaya gashi nan ynz zai zo ya dauko ku kuna daidai ina ne? Ya kwatan ta musu. Nan da nan aka qira driver ya tafi dan dakko su yazeed..  Jin sun taho ne alhj sanusi yace ayi breakfast kafin su karaso. Sai muyi duk abunda ya dace. Ba gardama nan akahau ciye2 da shaye2 su ya isah kuwa sai satar kallan maryam yake dan kayan da tasa sun mata mugun kyau dan saida ta dawo kamar yar china  hghhhhh lol.




Deeny kuwa gudu yake kamar me dan tsabar gudu ko gaban sa baya tsaya wa kallo daga ya juyo sai ya ga kamar karan zai kama kafar sa sai ya kara wuta. Sanda suka share kusan raibin sa'a suna gudun tukwana deeny ya waiga yaga ba karan. Sannan ne ma ya lura da wai har ya kawo bakin titi gaskiya ko shi yayi mamaki domin yanda ya tuna irin nisan da sukayi. Tsaye yake bakin titi ya kai 20mnt a gun baiga ko wuce wan mota daya ba. Tukwanan ya hango fitulun mota ta nufo inda yake kamar ya gudu ko me ya tuna kuma sai ya tsaya. Motar in police ne yaga ta farka godiya yayi ga allah a tunanin sa ga masu taimakon sa nan sun kara so.

 Abun mamaki  wani kurtu en sanda ne ya fito dauke da qulkin a hannunsa bai tsaya wata2 ba ya fara kwadar deeny a kwabri yana fadin sir daga ganin wannan mugu ne shi kuwa deeny da yake ta faman kare duqa kira yake wllh yallabai ni ba mugu bane ka saurare ni yallabai.ai ina kawai kwadar sa yake sanda suka mar likis tukwanan suka daukar suka jefa sa a bayan mota yan sanda uku ne 2 suka hau baya wato inda deeny yake dayan kuma yayi driving nasu.. Basu zame a ko'ina ba sai a office in su....  ayya srry deeny.




Tuni driver ya kawo su. Hk suka nufi cikin gidan gadan2  yazeed ne yaji kirjinsa na bugawa da sauri2 ya rasa dalilin hk gashi kuma sai karuwa abun yake. Su hjy saratu ne a gaba. Wato alhj a gabanta shi kuma yazeed bayan umman nasa. Baban yazeed ne ya fara shiga da sallamarsa. Gaba daya yan cikin parllon du idanu sukayi kan door. Ganin mai shigowa ne yasa ahj sanusi washe baki yana  wata kalan dariyan farin ciki. Sanda du suka shigo. Yazeed tsayawa yayi tsitt  yana kallan wani abu. Sannan gaban sa na dada bugawa  da sauri.



Halima ce da maryam yake kallo shi kam abun gani yayi kamar a mafarki. Sanda ya ji tna gaida su abban nasa sannan ya tabbatar ita ce ba mafarki yake ba. dama haleema na raye dama su mugu karya suke ashe basu kashe haleema da maryam ba. hmm tabbas bai cancanta su mugu su kara koda 1second a duniya ba. ko gaishe da su abba bai tsaya yi ba direct dakin sa ya wuce bai ko kalli su abba ba ya shige dakinsa dake a gidan. ................... Turkashi   yo ai hikenan


good night to oll my fans


King boy ne

Bi wannan line din domin join na grp dinmu

https://m.facebook.com/groups/1232550283531628












🔫.BANI NA KASHE TABA 😫🔫.



  Na big boy isah


.  *DEDICATED TO YOU 5STAR ✨✨ ASSOCIATION*

.


5 star's ✨✨ online writer's association 👌


.
Part 37







Yana shiga dakin a fusace  ya duba cikin wata as schoobag ya dauko wata Pistol sanda ya bude ta ya arngen in bulet in sannan ya sakata a tsakanin bel din sa da wando. Hk ya sake futowa a fusace sannan cikin hanzari yaxo ya wuce har ya kama kofa zai bude sai abbansa yace: yazeed miye hk ina zaka kake sauri hk ko gaida abbanka bakayi ba.dady ina zuwa kawai abunda ya fada kenan bai jira wata amsa ba ya bude kofa ya futa.  Gurin motoci yaje yasa key in motar ya warce ta kamar wanda zai tashi sama....ko ina zasa oho.





Deeny kuwa cikin cell na hango sa yayi tagumi duk an bubuge mar legs insa. Tunani yake tayi kala kala a zuciyarsa a gaskiya idan ya makara fa yazeed zai kai kawun haleema gidan can wato wa gunkin su. Shi isa du ya matsu da su sallame sa amma ina sunki wai shi mugu ne sai sunyi bincike a kansa. dpo suke jira kuma wai shi sai 9:30 yake zuwa.







Wani makeken gida yazeed ya parking tare da yin hoon mai gardi ya leko yana ganin yazeed ne da sauri ya bude gate in dake shima yasan yazeed. A millon ya shiga gidan motar bata ma  gama tsayawa ba ya bude morfin motar ya fito a fusace ya nufi cikin parllon. Ko wani knock bai tsaya yi ba. Ya tura door in ai kuwa ta bude. A dinner ya iske su mugu suna breakfast shayi da bready ne da wainar kwai sai indomei. Da suke ci. Ko sallama baiyi ba tsaye cik yayi yana kallan su. A zuciya yana cewa wato na baku aiki bakuyi ba kun min karya kuma gashi sai holewa kuke abunku.  Oga ne ya dago kai. Yazeed ya gani a tsaye ya zuba musu na mujiya fuska a murtike ba ko walwala a fuskarsa..

Ah mai gida yazeed barka da zuwa kana tafe ashe kuma shine ko call babu ai da mun tanadar maka special break da munsan zaka zo. Sai a lokacin ne su mugu suka lura ma da yazeed din take duk suka tsare shi da kallo suna mai wani dan murmushi wai farin cik...

Shi kuwa maganar ce ta ogan ta bata mai rai yaji wani tiririn bakin ciki yake ji a zuciyar sa. Wata zuciyar tace ya shooting insu kawai me yake jira da su wata kuwa zuciyar tace. Ya tambaye su yaji me zasu ce karya zasuyi ko kuwa..




Karku min karya. You tell me haleema and maryam was died?


Dukkan nunsu saida hantar cikin su ta kada domin duk sanda suka firfirgice  domin kuwa sun san tambayar nan ba a banza ba ruwa baya tsami banza kuma ga sun san yaxeed ba imani a tare da su duk shiru sukayi suka kasa cewa komai. Duk sun shiga saban thinking. Oga cikin sune ya katse tunanin da yin wani dan murmushi da gefan lips in sa suka dan bude kadan. Hmm oga yazeed kenan kaga ya daga hannu.'im kill Halima An m....

3 Shooting kawai naji sai dubawa nayi naga su duk a kasa waigowa nayi yazeed ne tuni ya juya da gun a hannunsa tana wani tiriri. Tuni ashe ya fusata ya sheqesu. (Sister nadis na juya  ina nema domin kuwa tunda akayi harbin banga inda ta nufaba a kasa na hangota shame shame ta sume ni kuwa da yake namiji ne dan fitsari ne shima dan tsirit ya kwace min a wando lol.)



Fita yayi  da waya a makale a kunnan sa : gud morng dad shi ne abunda ya fara furtawa dake mu Journalisms in zamani ne har mgnr wancan in naji. Morning hw ur day shine abunda yce: im 5yn: dad haleema an maryam they ar living. Me kake cewa kasan me kake fada kuwa.yes srry dad wllh  nayi da nasani sa su mugu aikin da ni na aikata da duk hkn bata faru ba amma saukin abu ba alamun cewa sun fadi abunda suka gani.gud ka take care of ur self. Ok dad bye. Ya kashe wayan sannan yi shiga motan sa yazo gate yayi oda da nufin mai gardi yaxo ya bude mai gate amma ina yaji shiru.


Abunda bai sani ba shine mai gadi yana jin shoot yayi waje da gudu. Dole ce tasa sai shi yazeed ya fito a motan yaje ya bude gate in. ( ni kuwa nace wa sis nadis ko dai mu tsaya mu bincike komai nq gidan ne domin kinsan wannan yan daban barasu rasa kudi ba a gidan nan nasu. Hannuna ta kama taja ni da karfi wai mu tafi bangaran deeny.Ni ce kash ynz gidan nan shikenan hk za'a barsa ko a group in nan akwai mai so?  Lol?






Can gidan su haleema tuni an gama breakfast kowa ya kama harkokin gaban sa su alhj bangaran su 1 su uku yau dai kawu an kashe mai zuwa kasuwa du da yaso ya fita amma hk bai samu ba su alhj sanusi sun hanashi dole tasa shi hkr. Yanayi yana musu surutu a zuciya hmm wato ku masu kudi ko kun tara ku bar bawan allah ya fita ya nemo na kansa amma kunki ku barni..



Hk shima isa yayi niyar jan yar kanwar sa su nufi gida in yaso sai ya dawo batun mgnr auran merry amma  alhj ya hana yace dole ya bari sai gobe domin akwai special gifts da zaiyi mai na ban mamaki. Hk ya hakura  gashi aliyu ma ya fita ya barsa shi kadai ne a wajan yayi zuru sai kale kale yake dake a garden ne. Ji yayi an rufe mai ido daga baya da wasu tatausan hannaye wani sanyi ne yaji ya ratsa duk kanni jikinsa. Baiji anyi mgn ba murmushi kawai yayi tare da cewa hmm sis anneey.... To na gano ki. Shiru yaji ba'a tanka ba kuma sai yaji abun zobe a hannun nan ya tabbatar da ba anney bace domin yasan ita bata da zobe............
Yo ay hikenan

good Morning to oll my fans


King boy ne

Bi wannan line din domin join na grp dinmu  ko ka/yi  search insa BIGBOY ISA NOVELS

https://m.facebook.com/groups/1232550283531628












🔫.BANI NA KASHE TABA 😫🔫.



  Na big boy isah


.  *DEDICATED TO YOU 5STAR ✨✨ ASSOCIATION*

.


5 star's ✨✨ online writer's association 👌


.
Part 38





Wata zazakar murya ce yaji ta daki dodan kunnan sa wace ta shiga cikin kwakwalwarsa ta inga mar yawo. Tabbas baxai taba mantawa da zaxakar muryan maryam ba wace tama zarce sarewa a gare sa. Hmm my merry yace. A cikin sexy voice insa wace ta haifarwa da maryam in wani kasala. Hmm taya ka gane nice lokacin da ta sake shi tana zagayowa ta zauna a bench in da yake a zaune. Hb tayaya ne zan ji muryan abar so na in kasa gane wa ai da bakiyi mgn bane shine sai in kasa gani wa. Smile yayi tare da cewa ya isah baka gayawa su umma abunda ke tsakanin mu ba kuma dazu kake cewa wai zaka tafi. Dan marairai cewa yayi tare da cewa ai ko na tafi ma to annesah zan kai in dawo gare ki sahibata. idan ka aure ni a wane gari zamu zauna.


Tabbas ta debo babbar mgn. Shin ynz shi mema zaice mata ne yasan shima kansa ba san zaman wancan kauyen yake ba balle ita da take dama yar birni  kai gaskiya dq sake to ynz ya zaka ce mata. Yna cikin yan sake2 ne.yaya isah  shine ya dawo dashi daga duniyar tunanin da ya afka. Yaya isah ina sanka so na gaskiya kasani cewa ko a village inku zamu zauna xan aure ka ya isah.


Wani murmushi yayi wanda ya kara bayyano kyawansa. Baice komai ba kallan ta. Hada ido sukayi sun dade a hk suna kallan juna. Hmm a hk dai na barsu..





Yazeed ne ya shigo ya park motan sa kafin ya fito sanda yayi control in kansa sbd tsaro da murmushin sa ya fito ya nufi inda su abban suke ya gaida su amma da kawu wato baban aliyu sannan yake gayawa abban sa ya shirya ynz zasu je domin yaga gun aikinsa da kuma mai gidansa. alhj bashir ya kalle sa yace to ai a shirye ma nake yi sauri ka zo mu tafi. Amma ina kaje ne naga kana hanzari hk ko karyawa kuma bakayi ba ka fita inji dadyn nasa.

Dady naje wajansa ne domin  ya kira ni namai wani dan aiki ne. Ok to allah yama albarka tashi jeka. Tashi yayi ya nufi parllo. Haleema da maryam da anney su duk ukun suna zaune a parllo sun kunna kallo sunayi hade da hira sama2."

Baima bi ta kansu ba direct room dinsa ya nufa. Ina kwana. Ya yazeed. Yaji ance. Juyowa yayi bisa mamaki yaga ai haleema ce. Lfy lau yace har ya juwa zai bude dakin ya karaji. An gaida shi da murya biyu. Maryam da anney. Ne suma hk dai ya cije lips nasa ya amsa. Sannan, ya wuce dakin nasa  kan bed insa ya haye yana jin wani tiriri da zafi a zuciyar sa""

Wanni bangaran kuma tunani yake taya zai hallaka su tun kafin su tona mai asiri domin tunani yake sun san ko shi waye. Amma yayi mamaki da basu fadawa kowa ba. Hakan yaji kmr ya kyale su hallarcin da suka mai na kin tona mai asiri. Saidai kash!! Lokaci ya kore dole ya kashe su domin kuwa a duniya banda su ba wanda ya san ko shi waye sai yan kungiyar su.


Mutanan gari a yaro mai ladabi  mai girmama na gaba da shi. Mai kyauta. Da san addini .da Kyakyawar tarbiya kawai suka sanshi. Ba wanda yasan mugun abunda yake aikatawa. Kuma ya shafe sama da shekaru 4 a cikin wannan kungiya. No! No ! I'll kill them     Necessary. Domin nasan ko ba yauba u can show my Secret.

Dan hk ya zama dole in kashe ku."

Tashi kawai yayi rai a bace. Ya fito da phone nasa yayi Dial in wata number. Hup ur ar ready cus I'm coming with my father.   Yes we ar ready" kawai a ka fada ya tsinke wayan ya shiga toilet in dake cikin daki . yayi brush tukwanan ya dan watsa ruwa ya fito ya chanza kayi. Jeans baki yasa. Sai wata riga T-shirt  mai lines blue. An white. Yayi kyau sosai sanda ya taje hairs insa yayi kyau sosai tukwanan yake fitowa a dakin.


Su haleema da ke xaune a parllo suna shiriritar su. Tun kafin ya karaso gunsu kanshi ya cika su. Gaba daya kamar hadin baki suka juya suna kallan sa shi kam ko damuwa baiyi da su ba ya wuce outside abunsa.  Haleema kam yayi mata kyau yau. Tace wa maryam kinga mutu yau anci gayu ko dai zance zashi. Kinga ba ruwana kinsan dai halin mutumin ... Hhhhh dariya halima tayi au ashe baki manta ranar ba. Maryam ta kama baki tare da cewa hmn wane ni in tuna.Anney kuwa tambaya ta shiga yi wai me akayi wancan ranar. Suka share ta. Domin Domin su shiriritar su suke  yi sai can halima ta dago ta kalli anney"" ohh sorry sis anneesat aniyi fishi kiyi hkr wllh we ar enjoyed.😜  bt bari in gaya miki abun da ya faru wancan rana🤔...."


Kamar kullum duk weekends maryam na kawo min ziyara ko ni in kai mata............ .........💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽  👑king boy 👑na gaisuwa


Bi wannan line din domin join na grp dinmu  ko ka/yi  search insa BIGBOY ISA NOVELS

https://m.facebook.com/groups/1232550283531628












BANI NA KASHE TABA 😫🔫.



  Na big boy isah


.  *DEDICATED TO YOU 5STAR ✨✨ ASSOCIATION*

.


5 star's ✨✨ online writer's association 👌


.
Part 39


HALIMA TACI GABA DA BAWA ANNEY LBR:
Ranar wata Sunday maryam ta kawo min ziyara:
Kamar yanda kika ganmu yanzu to hk muka zo parllo muka kuna kallo sai hira muke abun mu kasan cewar gidan ba kowa: haka yazeed yana gidan wato ya kawo ziyara:

Maryam ta tambaye ni miye tsakani na da yazeed da muke faman fada da shi hk. Nace mata wai kawai dan na shiga dakin sane kinsan ya hana. To miye a dakin wai shi da yake hanawa naga dai ba komai ne a dakin gwaro ba daga kati fa sai jakansa. Inji maryam. Nace mata to shi wannan ba hk yake ba domin shi abubuwa sunyi yawa a dakim nasa domin hada wani abu na gani ma a rufe da wani zane. Hk nake gayawa maryam a lokacin: ita kuwa kin ganta nan da karan bani tana jin haka naga ta mike..

Nake tambaya ina zata: tace wai dakin ya yazeed. Wai in taso muje tunda baya gida nacr mata wllh ni bazan je ba kuma kema ban goya baya kije ba idan kika je duk abunda ya same ki toh no my water inside: tace ita dai wai yaseen sai taje ta bincike dakin taga wai miye da yazeed baya san a shiga.:

Ai kuwa kamar wasa maryam ta nufi dakin ya yazeed ni kuwa kallo ya dauke min hnkali ;

Ban kula ba har ta bude dakin ta shige ba tare da fargabar komai ba domin nace da ita baya nan. Nidai ina nan sai kallo na nake nama manta da maryam ta shiga dakin."

   Ita kuwa bincike2 ta hau yi chan ta hango laptop insa ai kuwa taco sa'a ba password a jiki hk ta haye mai kan bed ta ta dane2 abunta."


   "Ganin shiru shiru maryam bata fito ba yasani tashi na bita abu mkki a kan katifa na ganta da kwampyuta sai wangale baki take bata ma ko kula da na shigo ba hkn yasa naje da sauri ke maryam wai me kike yi ne hk kinzo kin wani zauna a dakin mutum bayan kinsan idan ya dawo ya tarar dake sai ya wulakanta ki gashi kuma kinsan mum bata nan wllh duka xai miki. Yayin da nake karasa wa wajanta.ta dago min wani pic dake jikin laptop in ya yazeed ne cikon wasu red clothes wasu iri fuskan sa du ya shafe ta da wasu zane2 bt duk da hk yayi kyau abunsa bisa mamaki nima na biye mata."

 
    Nan muka yada xango a kan bed insa muke ta kallan pictures insu shida wadan su abokan su. Mun kusan share 30mints muna kallan pics in amma bamuga karshen su ba hk yasa muka koma wani bangaran. Da nace aje videos amma Maryam kwata kwata taki amincewa. Hk yasa na kyale ta badan naso ba ta kamo games nan ma mukata bugawa ni dai na nace a kan sai an shiga videos nashi. Uwar naci kin cika naci da yawa wllh ke da almajira ce da masu house sun shiga uku wllh. Bari a shiga videos in"
   

Mu kam sai shagalin mu muke yi ba ruwan mu mun ma manta da a dakin wa muke bamu damu ba mun sha'afa. Nan maryam ta nufi folder videos ni kam nayi mamakin yanda ta iya computer hk ma domin nasan bata da hkn yasa na tambaye ta a ina ta koya tace a laptop din yaya deeny mana. Direct ta shiga bude videos. Video farko ya ruda mu gaba daya jikin mu ya fara rawa a tare tuni muka kankame juna domin kuwa abunda muka gani ne yafi karfin tunanin mu...


  "' anney tayi zugum ta saki baki sai sauraren lbr take yi. Gani tayi halema na waige2 sanda taga ba kowa sannan tace.   "" ta yi kasa kasa da murya sosai sannan take cewa anny wllh in gaya miki annesah yazeed ne a videon ya rike wuka yana yanqa mutum. Kuma dan yaro Gashi nan jage2 duk jini shi kuwa sai yanka sasan jikin wannan yaran yake yaro ne fa dan shekara dudu baifi 7 old years ba. Ganin hk ya firgita mu da gudu muka tashi a tare ni da maryam da niyar muyo waje.ko laptop in baku wani tsaya kashewa ba abun mamaki. Ina kama kofar when ya yazeed shima ya turo da niyar xai shi go'"


  Karki so kiga yanda mukayi baya a wani firgice ni kam bansan
Lokacin da na shiga basa hkr bama maryam kam tuni ta tsorata tama fara kuka. Shi kam da ya shigo tsayawa yayi chak ya kare wa dakin kallo yaga duk an bincike mar daki can ya hango laptop dinsa a kunne tana kallo.  Daga jin sautin video  ya gane ko wanene. Hk yasa shi kulle dakin da key ya kuma can gefan katin fansa ya jawo computer ya kashe tukun. Ya hada hannuwa biyu ya dara a goshi alamun yana tunani kenan..

    "anney in takaice miki lbr wllh ranar  mun daku domin samun mu yayi kamar yayan sa ya dinga lafta yana fadin zaku kara muna kuka muna aa sanda yayi mn dukan tsiya sannan yace muyi shiru. Ya zazare mn ido tare da cewa wllh muka sake muka kuskura wannan magnr ta fita duk sai ya kashe mu kuma duk sai ya yaya kammu.  Hakika mun tsorata.
   
   
       " ba yanda muka iya hk ya bude mn kofar muka dawo parllo muka sha kukan mu tukwanan du da hk sanda ya dawo ya kara mn kashedi a kan karmu kuskura zancan nan ya fita.
   
   
      " kinga zancen nan dana fada miki ko to wllh  ba wanda na fadawa ko ummana da abbana basu sani ba domin nasan wannan mugun zai iya aikata komai. Halima da tazo nan ta juya ga maryam. Ke ko kin taba gaya wa wani. Ni wace ni ni nama isah. Inji maryam. Ai tun lokacin na kama baki na nayi shiru gidama da naje mama tayi kokarin gane miye ya same ni amma naki fada mt nace ba komai.  Anney ta rike  baki tare da girgiza kai chabb!! Wllh idan nice sai na tona asirin sa a kan me. Ke rufawa kanki asiri idan kika fada akaje kuma ba'a kama sa da hujja ba ya xaki ce?
   
    Jikin anny yadan yi sanyi. U see ba muda mafita ne. Kawai kedai ki bari rana dubu ta barawo rana daya ta mai kaya  ko ba hk bane. Hk ne inji anney sannan ta miki matar yaya xo ki dan rakani mn .inji anney take fada mawa maryam. Maryam ta mikr tare da cewa ina. Dakin yazeed mn da sauri maryam ta  koma ta zauna tare da cewa ba dani ba. Ai  kuwa duk suka kyalkyace da dariya."
   
   
    Deeny kuwa yana can sai fargaba yake shi kam yama rasa me ke mai dadi domin yasan jiki rinsa nada mumunan hatsari indai har yazeed ya sama damar tafiya da abban sa wancan gidan tabbas akwai matsala. Domin kuwa dodansu za'a bawa shi.   Gashi yawa yan sandan nan bayani amma ina sunki sauraran sa wai kawai basu yarda dashi ba muna fiki ne.
   
    Shigowar dpo ce ta dansa zuciyar sa ta danyi sanyi............................gud morng
   
   
   
🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽  👑king boy 👑na gaisuwa


Bi wannan line din domin join na grp dinmu  ko ka/yi  search insa BIGBOY ISA NOVELS

https://m.facebook.com/groups/1232550283531628
   















BANI NA KASHE TABA 😫🔫.



  Na big boy isah


.  *DEDICATED TO YOU 5STAR ✨✨ ASSOCIATION*

.


5 star's ✨✨ online writer's association 👌


.
Part 40








can yaji shigowar dpo hkn tasa ya sama yar natsuwa. sanda suka mawa dpo in bayani tukwanan ya nufi wajan deeny. shi kuwa dama kamar shi yake zuwa yana isa deeny ya gaida shi ya amsa tare da karewa deeny kallo. kai gaskiya wannan ba mugu bane hk ya fada a zuciyar sa. tare da zuwa gab da deeny ya tsuguna a cikin cell din.


    " kalle ni nan ina so ka fada min gaskiya who ar u? 

     deeny da hawaye tuni sun cika mar ido ya fara bayani  sunana zahradeen kaza da kaza dai ya fada mar kaff labarin sa har mutuwan halima dama yanzu tserowar sa . dpo ya yi wani gwabran nunfashi sannan yawa deeny wani kalan kallo yace. do u sure? dpo ne ya tambaya deeny.    yes am sure sir.  i can't tell u lie.  ok yanzu kace yazeed ya bayar da mahaifin sa mawa dodo ko? kwarai da gaske kuma yallabai jinkirin mu ma ba karamin hatsari bane ya kamata muje ka tabbata da kanka.

    bai gardama ba yace a kunce deeny. wani kurtun dan sanda ne naga yaje ya cire mai aunkwa din dake sanye a hannunsa.  sannan dpo din ya dauki mutum 4 daga cikin yaran sa banda shi da kuma deeny. suka hau mota dirct suka nipo gidan su haleema.  shikam deeny godewa allah yake tayi da dpo nan ya fahimce sa. a zuciyar sa da yana  tunanin ko dpo in mugune amma ynz kam yaga sabanin hk..



yazeeed kuwa yana fita daga parllo ya nufi gun da su dad insa suke a xaune su uku ne suna hira. wato da baban sa da kuma wan babansa sai kuma baban aliyu wato kawu. hk yaje cikin ladabi (kunsan ance mai san kayan ka yafika dabara) yaje ya sama dad insa yace dad na shirya. ok mu tafi kenan a cewar dadyn  yauwa ai kuwa ina ganin gwara kawai mu tafi mu duka tunda kaga wadan nan suma iyayan ka ne ya nuna su kawu.  lokaci daya yazeed ya bata fuska yaji ana shirin bata mai plan.  aa dady kawai gwara dai mu tafi mu biyun kasan mai gidan nawa bai cika san hayaniya da yawa ba. abban haleema ne ya kalle sa tare da mai dakuwa uku ka nace wato mune zamu mai hayaniyan ko to dai mu nan duk uwayan kane kaji na gaya maka.  sun kuyar dakai kawai yayi. wayar alhj sanusi ne tayi kara ganin wanda yakira ne yace to ni ga ma kira ya shigo wayana kuje kawai domin wani abokin kasuwanci nane kuma zamu dade muna waya.  ahj bashir ya tashi yana murmushi to ai shikenan bari muje yanzu zamu dawo isha'alah.  suka nupi motar yazeed ya hau sannan aka bude musu gate suka fita.



can bangaran kuma isah ne shida a liyu a zaune da yake gidan fadede ne kowa harkan gaban sa yake yi. suma hk zaune suke suna hira nan aliyu yake tambaya ko an zabawa anneesat miji ne. isah kuwa yayi farin ciki da wannan zancen domin kuwa yasan ba a banza aliyun zai mar wannan tambayar ba.
  "aa ba wani tsayaye ko a can kauyen ma"  gud. aliyu yace yayi shiru kuma. ko da wani Abune  isah ya taimbata. aa wllh ba komai kawai na tambaya ne.  hmm to shikenan tunda kaki fada .



jiniyar motar police suka ji ta parka a kofar gida nan take dpo ya fito ya sako deeny a gaba  sukayi slma suka shigo gidan mai gadi kam da yaga police ne kuma ga deeny a gaban sa yayi mamaki sosai na ganin deenyn. hk shima kawu ya mike yana kallan deeny duk gaba daya matan dake cikin gidan du sanda suka yo waje maman deeny kuwa suman tsaye tayi dan farin ciki na ganin yaran nata amina ce tayi kanta a kidime. ba tare da bata lokaci ba dpo yaje ya bawa alhj sanusi hannu suka gaisa sannan yabawa kawu ma deeny kuwa idan sa a kan mahaifiyar sa yake wanda yana gani ta zube ta wane fanni a tsorace yake"


  kwayar idansa ce ta kai ga masoyiyar sa wato halima al'amarin da yayi matukar bashi mamaki kenan'  shin wai wannan halima tace ko dai idona ne yake min gizo sanda ya kara sa hannu ya murza idan don ya tabbatar da hkn. bai tabbatar ba saida yaga ana ta faman citan ummansa da ita.   alhj fatan dai kasan wannan yaran a gagauce.  kwarai kuwa wannan deeny kenan shi muke ta faman nema ma a hlin ynz.  alhmdulilah inji dpo a hlin ynz ba lokacin batawa ina yazeed da kuma abbansa. yazeed ai ynz suka tafi







Inalilahhi wa'ina ilaihi raji'un 2  su deeny suka kama fadi ba'ayi wata2 ba suka juya tare da cewa alhj ya biyo su ynz ba lokacin yi masa wani bayani. Cikin sauri suka hahau mota dpo in shike driving Nash














BANI NA KASHE TABA 😫🔫.



  Na big boy isah


.  *DEDICATED TO YOU 5STAR ✨✨ ASSOCIATION*

.


5 star's ✨✨ online writer's association 👌


.
Part 41








innalilahhi wa'ina ilaihi ra'jiu abunda ke fitowa daga bakin su deeny kenan. ya kara nana tawa ya tafi.officer yace alhj zamu iya tafiya yi sauri biyo mu ba lokacin batawa'" lfy ya fara tambaya.  no alhj lfy lau jinkirin mu shine zai zama ba lafiya ba. da sauri alhj yabi bayan su inda su kuwa tuni sun juya nufi motar su. wannan karan ma dpo ne ke drivering nasu deeny kuwa na nuna mar hanya. a 360 suke gudu dake sun saka jiniya shi yasa motoci ma basu hanya suke. 

can sunyi nisa sun kusa fita da gari sai suka hangi motar yazeed sai uban gudu yake ba saurarawa. da dpo yayi niyar suje su tare sa amma. deeny yace kar ayi hk gwara dai aje har gidan nasu a toyashi ma in yaso dama akwai yan sandanku da aka hadani dasu biyu na nan amma dayan wato ogan su tuni an  yankasa. innalilahhi kawai dpo ya fada tare da cewa allah ya gafarta mar. a nan ne alhj ya dan fahimce su yake tambaya su fada mai me ke faruwa ne.


"dpo ne yace yayi hkr a ynz ba halin yin hakan a hankali suke bin bayan motar yaxeed shi kam baima lura da wata motar police ba da yake ya dan basu tazara."   abban sa kuwa gani yayi ana taba tafiya dashi har za'a bar cikin gari a yanki daji amma ba'a zo ba. kai yazeed wai ina ne nan zaka kaimu"  dad ai mun kusan karaso wa ba nisa.  can bayan sun sake yin wata tafiya mai dan nisa dady ya kara tambaya domin guraran shi baiga alamar gari bama. dady nace ka kwantar da hankalin ka mun kosa zuwa"  kai bana san shirme wannan wace kalar shiririta ce tun nan baya da 20mint kace min ankusa zuwa sai ynz ka kara cewa an kusa. kaga ni bansaka dole ba in dama karya ne kake min baka da wani uban gida to gwara ka fada sannan ka juya mu koma domin ni zaman motar nan ba wani kaunarsa nake ba. im very tired.  ganin baban nasa zai kawo mar matsala ne yasa shi fiddo da wata yar kwalba ya fisa mar. ba'afi 30sec ba abban  nasa ya hau barci ba kakaftawa..



  su kuwa su deeny a baya suke suna biye da su. deeny ne yake bawa  dpo shawara a kan a karo ma'akata  in so samu ne har sojoji ma a kira wo domin na tsorata da kalan kartan wajan.   dpo yace hmm deeny ke nan zaka nuna mana aiki mune. aa yallabai ni kawai shawara na bada. kafin deeny ya rufe baki ne suka hangi motan yazeed can zata gangare daga kan titi.  ta nufi wani daji.

  nan ne fa dpo ya fara gaskata maganar deeny  nan take  kuwa yasa a kira babban office dinsu dake nan cikin garin kano ya bayyana musu abunda ke faruwa tare da fadi musu address in gun da suke a yanzu. sanda suka bari can yazeed ya mika tukun suma suka gangaro motar tasu suka bi bayan sa shi kam duk abunda ake bai ma san akwai mota na biye da shi ba. dad sa kuwa nan ya kwanta ya dingi barci na fitar hankali..

   bangaran maman deeny kuwa da aka dauke ta aka kaita daki suman da tayi. bayan tafiyan su deeny kadan ta farfado ba abunda take kira sai.  deeny2 ashe dama kana raye ina ka tafi ka barni. duk wanda ya ganta a wannan halin tilas ya tausaya mata ko dan domin abubuwan da take fada nan ta fara cewa wai ina deeny ko dai dama idona gizo yake nuna min ne. maryam ce ta ruko hannunta aa itama hawaye take. itama sai lokacin ta fahimci ashe yaya deeny baya gida boye musu ne kawai akayi. mama kiyi hakuri sunje su dawo tabbas deeny ki ne. nan dai suka shiga lala shin ta. haleema kuwa wane farin ciki take na ganin sahibin nata ita kam gani tayi ma ya kara kyau yayi haske yama fi da. hakan yasa ta. tashi ta tafi dakin ta ta fada kan bed sai wani kukan dadi take. nan ta hau thinking in sa....


aliyu da kawu kuwa duk hankalin sune ya tashi sun rasa abunyi.  ba'a musu bayanin abunda ke faruwa ba. "malam nifa ina jin kamar ba lafiya ba ace har ynz su  anney basu dawo ba. ni kam ba babana nake jiwa ba domin ai shi namiji ne zai iya zuwa ko ina ba tare da wata fargaba ba amma ita fa anney ita nake ji malam.

  haba ke kuwa zuwaira me yasa kin cika garaje ne kuma ke da zaki dinga musu addu'a ai addu'a  zaki yi ba ki tsaya ki dinga zarge2 ba kinsan dai isah yaro ne mai natsuwa bazaiyi abunda zai saka mu a damuwa ko ya bata mn raiba. ni banyi tunanin zai kwana a can bama to amma kika sani ko lokacin da sukaje dare yayi ne kuma iyayan yarinyar suce sai sun tsaya sun kwana.'"  to allah dai yasa a dace kuma allah ya kare mn su.  ameen kinga da tun farko ma haka kika ce.  to ai malam abun ne da ban tsoro yanzu fa kaga karfe 10... da wani abu amma, yaran nan basu dawo ba.  ki kwantar da hankalin ki zasu dawo isha'allahu ya fada lokacin da yake mikewa. to ni zan fita kuma sai na dawo zan biya wajan kaka daga nan in bata sako domin kinga jia an barta ita kadai a gida.  to malam allah yasa a dace a gayar min da kakar. to zata ji isha'allahu... 




yazeed na gaba suna binsa a baya can da suka hangi gidan kuma suka lura nan ya dosa sai suka kara gudu wato dan su isko sa. amma ina tuni ya riga ya karasa domin ya musu nisa. a guje suka karasa. tun kafin motar ta tsaya yan sanda suka fito kowa da gun a halannunsa. suka nufi gidan.  nan deeny kuwa ya shiga gayawa abban halima abunda ke faruwa...............

good  morning oll my frnds 🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽  👑king boy 👑na gaisuwa


Bi wannan line din domin join na grp dinmu  ko ka/yi  search insa BIGBOY ISA NOVELS

https://m.facebook.com/groups/1232550283531628









BANI NA KASHE TABA 😫🔫.



  Na big boy isah


.  *DEDICATED TO YOU 5STAR ✨✨ ASSOCIATION*

.


5 star's ✨✨ online writer's association 👌


.
Part 42










abba yayi mamaki sosai ya jinjina kai zuciyarsa cike da tunanin irin wannan yaro wato yazeed duk biyayar da yake wa abban nasa karshe kenan  dama duk kudin da yake da su ta hanyar da ya tara su kenan.  banyi tunanin yazeed zai iyawa yaya hk ba ban ma taba tunanin yazeed zai iya kashe ko kwaro ba balle ma ace wai mutu. hmm ko da yake dan adam ne. abba to ai shine yayi yunkurin kashe su haleema ma da bakinsa naji yana fada lokacin da nake a tsare a gidan. inji deeny. ya allah.abban halleema ya fada tare da dafe kansa da yaji yana irin wata juywa dama yazeed fadan da suke da halima ba iya nan ya tsayaba yanzu ita daya tal da nake da ita yayi niyar hallaka min kai amma da ya cuce mu gaskiyq a duk family's namu baxa mu taba yafee wa yazeed abunda ya aikata mana ba allah ya isa tsakanin mu da kai yazeed.

  " direct gate din gidan suka nufa cikin irin sallan su na ma'aikata wanda suka san aikin su bibiyu suka kasu inda shi kuma dpo ya bi bangare daya daga cikin su a hankali suka tura gat din guda daya ne ya fara kutsa kai can ya hangi motar can amma wayan ba kowa a cikn ta . nan ya daga wa na waje hannu a lamun su shigo bayan ya leka ko'ina baiga kowa ba. haka suka shiga a hnakli suke tafiya cikin sandobda tako nasu irin na ma'aikata . wani daga cikin sune ya tura dakin sa kafarsa keda wuya sai sukaji shoot anyi harbi ba dan yayi gagawar dukewa ba da sai ta same shi da sauri yayo baya.  sunyi mamaki matuka ta yanda akayi yazeed ya san da zuwan su shin dama ya gansu ne ko kuwa. hkn suka fara tunani..



BAYA... 

yazeed tunda yaga abba ya fara barci ya fara tukin sa a hankli kwance yake tuki abunsa. can ya lura da motar police amma kawai sai ya basar a cewarsa ai shi ba wani laifi yayi ba me ruwansa da su kuma ma dan yaga tabbas din hakan sai ya dinka rage sauri domin wai suzo su wuce du dadai can nesa da shi suke abun mamaki kuma du sanda  ya rage gudu suma sai yaga sun rage haka  dai ake ta tafiya ana cikin hakan ne yaji wayan sa na Ring yana dubawa yaga dad wato wancan dad in nasa matsafi nan yake fada mar cewa daya daga cikin wa'inda muka kamafa ya gudu yazeeda yace garin ya bayan ba wanda ya taba guduwa daga cikin gidan nan ya haka ta faru. dad din yake gaya masa cewa ko ka manta ne sai wanda yaci abincin gidan ne bazai iya fita ba to yaran taurin kai ne da shi ba yanda bamuyi da shi ba a kan yaci amma yake. ok dad yanzu miye abunyi domin ga wata motar police nan ina kyautata zatan kuma ni suke bi to amma ni bansa ya akayi ba domin ni kam ban karya dokan titi ba tun tahowata.  ok kadai kara kula kuma ka lurs sosai yanzu kuna tare da dad din naka? tsohon ya tamabya"    eh muna tare gashi nan ma wllh sanda na sa mar powder barci tukwnan domin naga ya fara ganowa. ohhh sbd me kasa mar ai da baka sa mai ba domin kasan dokar gunki mu bazai karba kyautan nan ba ko kuma zai raina ne anma da ka kawo shi a hk kasan fa muna da kartai ko da karfi ne da sai mu turasa ga ogan. srry dad ai ina tunanin ma kafin in karaso ya tashi domin bamai karfi bace sosai. ok sai kazo be carefull " ok dad.



yazeed bai tabbatar da su deeny shi suke bi ba sanda ya shiga dajin nan can yayi nisa ya hango su suma sun biyo sa lokacin da har zai waske  yayi wani gun kuma sai ya fasa ya sake call in dad nasa ya sanar da shi cewa police din shifa suke bi. dad yace ba damuwa zasu shirya kafin karaso warsa kawai yazo ba damuwa. haka kuwa yaje ya shiga gidan ya park mutansa sannan ya kira wasu suka taimaka masa aka dauki dad da yake faman barci kamar  na mutuwa aka sashi daga ciki.


tuni karti gidan kowa yayi shiri tare da mugayan bindigun su a hannu. bt suna ciki wato a parllo ba su fito ba sbd tsaro.  can su kuwa yazeed da ogan tsafin sa kokari kawai suke na su tada dad wato alhj bashi domin su bawa gunki sa domin kar lokci ya kure dan idan lokaci ya kure basu bawa dodan nan abunda yake bukata ba duk sai sun moto a wannan ranar ba wanda zai tsira shi yasa ma basa wasa da du umarnin da ya basu. nan dai suke ta iya kokarin sa amma ina yaki ya farka sun kwara mar ruwa sunyi2 yaki ya farka balle su jefa sa cikin dakin dodan. suna cikin hakan ne suka ji anyi harbi hakan ya dada tabbatar musu da cewa yan sandan ne suka karaso. nan suka kara azama yayi tashin alhj bashi a baccin.



CI GABAN LBR...


su dpo kam da sukaga hk komawa sukayi da baya suna tunanin taya zasu jewa wannan mutanan gasu su biyar ne kawai hkn tasa ya sake Dialing in number shugaban su a kan suna bukatar taimakon gagawa fa. deeny da sirikinsa da aka bari a cikin mota ba abunda suke sai addu'a allah ya fito musu da alhj bashirlfy ba kamar alhj sanusi yanda ya damu shi kam kamar ma ya shiga da kansa dan cetan dan uwan nasa. su dpo kam jinkirtawa sukayi anan suna tunanin  wane tsari zasuyi dan shiga gidan nan kai saidai fa kuma mu biyar ne gashi bamu san ko su nawa bane a ciki sannan bamu san yanayin makaman su ba dole dai mu jira wa'ina aka turo mn su karaso.  wane police ne daga cike yake cewa sir baka tunanin zasu iya cutar da alhj kuwa idan mukayi jinkira.  to ynz ya kake tunanin xamuyi kasan fa cewa duk wanda ya shiga parllo nan sunan sa shekake domin kaga fa, yanda akayi harbi kalan karan gun dinma na daban ne ya kamata mu kula. good  night oll my frnds 🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽  👑king boy 👑na gaisuwa


Bi wannan line din domin join na grp dinmu  ko ka/yi  search insa BIGBOY ISA NOVELS

https://m.facebook.com/groups/1232550283531628








BANI NA KASHE TABA 😫🔫.



  Na big boy isah


.  *DEDICATED TO YOU 5STAR ✨✨ ASSOCIATION*

.


5 star's ✨✨ online writer's association 👌


.
Part 43










al'amarin barcin dady yazeed fa zuwa yanzu ya fara basu haushi to shi wai wane irin maganin barci ne wannan domin sunyi yan dubarun su na ya tashi amma ina har ruwa mai sanyi na frigid suka dinga kwarara mai amma ko motsi yakiyi hakan yasa suka shika mai allurai masu kashe wannan ta barcin amma ina shuru yaki ya farka hakn ya fusata wannan tshon shi isa yata dura mar allurai iri2 ba sasauci su  abunda ba su sani ba tuni ya suma domin sinadaran da suka hada mai sun yi yawa.  yazeed kam tashi yayi ya jigina kai jikin bango bakin ciki ya cika shi. kamar ya karasa kashe abban nasa yake ji sai dai ba halin yin hk... dole suka kyale sa suka nema gu suka zauna a cewar su saiya fardado..



su dpo ne hade da sauran yaransa sun tsaya sai zurga zurga suke domin su rasa abunyi. hk shima abban haleema addu'a kawai yake  shi baima iya daurewa ba sanda ya shigo gidan ya tambaya wane hali ake ciki yanzu shi duk a firgice yake kar a hallaka mar dan uwa wanda shine ya rage mai dan uwa na jini a halin ynz. aka sanar dashi cewa ya kwantar da hankalin sa ba abunda zai faru amma ynz akwai ma'akata da aka turo mn da su ynz sun kusan karasowa. sannan dpo yace dashi ya koma mota domin bamu san irin plan dinsu ba...


suna cikin maganar ne sai sukaji karan motoci hk ya tabbatar musu cewa ma'ikatan ne suka karaso hkn yasa gabaki daya sukayi waje. sojoji ne da police kuma kowannan su mota 5 cike da yan sanda da da sojoji cikin shirin yaki. hk suka fara dira  daga saman mota tun kafin a tsaya nan take duk suka zazagaye gidan inda su kuma sojojin da zasu kai kimanin 12 sune suka nufi cikin gidan sanda dpo ya musu bayani tukwanan suka tsaya suna tunanin yanda zasu biyowa da al'amarin.  ciki kuwa kato ne sama da 50 ko wane rike da mahaukaciyan bindiga yayi target na kofa lalai kam duk wanda yayi gangancin shigowa parllo in nan zai zama sheqaqe domin duk a lalabe suke a cikin parllan...


Command wa mutu 3 su shiga allah sarki da yasan me zai faru da bai aikasu ba. shiga sukayi kai tsaye cikin parllon cikin sanda da dabara irin tasu amma ina lokaci daya sai ganin mutun sama da goma sun fito kafin suyi wani yunkuri tuni an hallaka su duk da rigan bullet in dake jikin su.  tabbas suma kartin nan ba'a banza suke ba sunyi training mai kyau. sannan sun san salon yaki.


suna waje sukaji karan fitar harsashin  can kuma sai sukaji shiru ko motsi basu kara ji ba. hkn yasa aka kara umartan mutum biyu da su shiga. ba garma ma kuwa suma suka kutsa kai.akwakwance suka is iske abokan aikin nasu wannan yasa sukayo baya saidai a lokacin ne kuma sukaji kartan nan sun fara shooting nasu. nan dai suma suka fara kokarin mayarda martani hade da gocewa sun ci nasarar. harbin mutum daya. daga cikin kartan bt an kashe daya suma dole tasa dayan juyawa da kyar yasha. a tsiyace ya fito da gudu. nan yake sanarwa da  shugaban nasu irin shirinn motanan nan. ogan nasu yayi ajiyan nunfashi. yana tunanin ta wace hannya kuma za'a shiga gidan nan..


dpo ne ya kawo shawara cewa hanya biyu ne kawai dole a turo mn da kartafila ko kuma tank domin gidan nan saidai a shige sa ta hanyar rusawa haka ne kawai mafita.  no ba sai anyi hk ba inada abunyi.....



maman deeny kam tuni an rarashe  ta ta hakura ta dawo hayyacin ta sai dada godewa allah take yi na bayyana mata du ya'yan' ta bayan da har tama hkr da su.  kaddara kenan. maryam kuwa saida taga hnklin umman nasu ya kwanta tukun ta fito domin tana kewar ganin isah. tare da yaya ali ta gansu zaune a garden sai hira suke.  suna ganin ta suka fara tambaya ya jikin umma.  da fara'arta ta basu amsa umma kam jiki yayi sauki. ya aliyu ashe kuna nan. eh wllh sis maryam muna nan muna dan hutawa bakwan naku ne ya takura a kan wai shi tafiya zaiyi shine nake bawa hkr. maryam kuwa bata fuska tayi jin  ance wai ya isah shirin tafiya yake.to ya zaimin hk sanda ya sace min zuciya tunanin sa ya hanani sukuni zai tafi ya barni to in ya tafi ma yaushe zai dawo. maryam data sunkuyar dakai tana ta zancen zuci. ya ali yace sis yadai naga kin dan bata rai dan ance zai tafi ko dai bakwan sirikin mune ya fada cikin tsokana. dago kai tayi ta kakaro murmushi kai ya aliyu ka cika zolaya ni ina ruwana da shi ya tashi yata tafiya mn idan har zai bar mn annisat din mu.isah da baice komai ba har a lokacin kallanta kawai yakeyi yace ok hk kika ce ko to ai shikenan indai anney ce gata nan ai sai kucinye an bar muku. ya kalli ya aliyu lokacin da ya mike. bro tashi ka rakani in hau mota mn tunda kaga dai korar mu ake a garin naku. aa ba'ayi hk ba gsky mu kam mun isa mu kora sirikin mu ai mu bamu isa ba.  aliyu ya fada yana dariya. maryam  kuwa ganin aliyu ya gano komai yasa ta rugawa ciki cike da kunya tana dariya...


ohh kace kazo zaka dauke mana sis mu ko. aliyu yake zolayan isah. ai wannan abun baza mu yarda ba kuwa sai dai ayi chanje.  isah murmushi kawai yayi baice komai ba amma kmr ya so ya gane wani abu a cikin zancen aliyu hk shima aliyu yaso yayi mai mgn. domin ya tabbatar mai da cewa shi fa yana san sis sa amma sai yayi shiru. baiji dadin shirun ba.




shugaban sojojin nan kuwa wasu ya aika mota domin su kwaso tiagass....................

yo ai hikenan..good  morning oll my frnds 🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽  👑king boy 👑na gaisuwa


Bi wannan line din domin join na grp dinmu  ko ka/yi  search insa BIGBOY ISA NOVELS

https://m.facebook.com/groups/1232550283531628













BANI NA KASHE TABA 😫🔫.



  Na big boy isah


.  *DEDICATED TO YOU 5STAR ✨✨ ASSOCIATION*

.


5 star's ✨✨ online writer's association 👌


.
Part 44






👮🏻👮🏻👮🏻👮🏻👮🏻👮🏻

tiagass aka kawo inda shugaban ya bukaci kowa ya zo wato yan sanda da kuma sojojin nan ya fada musu wasu yan mganganu ni dake ina nesa da su dan tsaro😎 banji ko me suke cewa ba tiagass din nan naga an rarabawa wajan mutum 5 inda suka nufi kofar parllon direct tun kafin su shiga suka fara aika tiagass ta ko'ina na cikin gidan hade da wulla wani abu nan take dakin ya wani gauraye da hayaki ga kuma tiagass ba abunda kake ji sai tarin kartai inda suka fara jin nunfashin su na neman dauke wa hkn  yasa su kidimewa ko gani ya gagare su.daga jin hk masu harba tiagass din sai sukayi baya a guje ganin kartin sun fara yowa kofa. wow su kuwa yan maza cika sukayi da farin ciki. kuwa yayi target din gun insa. duk katan da ya fito sai dai wani  ba shi ba. su ka dingi fitowa a guje su kuwa yan maza na sakar musu harsashi ta ko'ina. kafin kace me an kashe sama da kato 30. su kuwa su yazeed da suke can dakin a lungu duk wannan abun da ake bai kai musu can ba. su ba abunda ya dame su illa kin fardadowar da dad yayi..


sojojin nan ji sukayi tsit kartan nan sun daina fitowa saidai ga wanda aka kashe nan birgik a bakin parllo. dpo ne yake bada command kan a afka ciki. shugaban sojajin ne yace wait ku dakata tukun nan. dpo a tsawace yayi mgn. taya zakayi stopped nasu bayan kasan zasu iya kashe shi a ko wane lokaci. shi kam shugaban sojojin sai lokacin ma ake sanar da shi cewa abban yazeed na ciki kuma zasu iya hallaka sa a ko wane lokaci. nan take ya fusata. ran shi ya baci. tiagass din ya dauka tukun ya saka wata hula da wani a fuskansa irin wacce suke sawa dan kare tiagass din nan take suma wasu daga cikin su suka sa har dpo shima yasa. nan ya bada command a kan wasu su tsaya wasu kuma su biyo shi ciki sannan yayi gaba. kallo daya zaks mar ka gane ba mutunci ba sani ba sabo..



kai tsaye cikin parllo ya nufa ya fara harba tiagass ta ko'ina sauran mutanan da basu fito ba ba arziki suka dinga fitowa su kuwa duk wanda ya fito ba dage sai a harbe sa hk suka ta fitowa daga mabuyarsu a cikin gidan nan. su dpo aiki kawai suke baji ba gani abun in kagani sai ya baka sha'awa. dakuna suka fara dudubawa a bude wannan aga wayam abude can aga wayam ana hana haka har aka kai ga wadan nan police din guda biyu gabaki daya an aske musu kai alamun dai an kusa asha romo su kuwa abincin da suke ci da naman mutu yasa su sunyi kiba sun wani kara kyau saidai daga ka gansu kasan sun fita a hayyacin su ba'a cikin hayyacin su suke ba nan aka hada su da soja biyu. domin a kawo su waje. sannan su kuma su dpo sukayi gaba suna ta leka dakuna...




sunyi tafiya mai nisa a cikin gidan nan dakuna ne sun kai 200 haka dai suka ci gaba da tafi ya a dakunan ba'a samun komai sai wani dakin aske jini jage2 wani kuma kayan mutane amma ba mutanan. a cikin tafiyan su ne har suka isa kitchen inda suka iske abubuwa a cikin sa ba kyan gani sasan jikin mutu kala2 na yara da manya mata da maza. nan take shugaban sojojin ya umarci wasu da suje su da dauko galuluwan petur su wawatsa a ko'ina na gidan ba gardama kuwa mutun 3 suka koma baya. domin ai watar da abunda aka umarce su...





wani daki suka iske wanda kofarsa ma shi wannan dakin ta babanta da sauran haka yasa suka yi tunanin cewa lalai a nan su yazeed suke nan take aka rarabu a hankali wasu left wasu kuma right. shugaban su ne ya umarci wani daga cikin su a kan yasa takalmi ya  tura kofan da yake a bude take kuws yana sa kafa ya tura da gudu suka na gefe gefan suka shigq ciki. yazeed da dadyn sa na tsafi a zazaune suke sunsa alhj bashir a gaba shi kuwa da har yanzu a sume yake. kafin yazeed yayi wani yunkurin fiddo bindiga tuni wani soja ya sa kafa ya bangaje shi can ya fadi. shi kuma ya bishi cikin hanzari ya danne .inda shi kuma wani police yazo yasaka mar ankwa. hk shima tsohon nan ba yanda ya iya aka mayar mai da hannuwa baya aka saka mar ankwa. su dpo kuwa kan alhj sukayi. wanda yake a sume da sauri dpo ya sabe shi da gudu yayo waje da shi inda a lokaci masu zuba fetur tuni sun zo gun haka aka daga dakin gunki ma saida aka mai sharaff da fetur sannan aka cinns mai wuta. da bissimilah. wani kalan kuka2 ne ya dinga tashi a ciki da wani hanani2 dai abubuwa kala2 nan aka tura kyayar su yazeed anayi ana ball da shi. kafin azo waje tuni an kunkumbura mai kafafuwa. dpo yana fitowa da alj bashi motan da su deeny suke ya nufa ya saka shi a cik bai ko jira ba ya hau motan yasaka jinia ya take motar da gudu. alhj sanusi da shine a kujeran baya inda aka saka saka baban yazeed jijiga sa yake yana kiran yay yaya amma ina shiru sai ma jikinsa dake dada yin zafi hk tasa shi juyowa a firgice yanawa dpo mgn a kan yayi sauri ya karasa hospital dan cetan rayuwar dan uwan nasa.

shugaban sojoji nan ne yasa yazeed a mota suka nufi Barracks da su. sauran police din nan kuwa sanda sukawa gidan nan kurmus tukun suka bar gun........................kuyi hkr da wannan am busy bt maybe gobe in karasa muku...    love u oll my frnds 🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽  👑king boy 👑na gaisuwa


Bi wannan line din domin join na grp dinmu  ko ka/yi  search insa BIGBOY ISA NOVELS

https://m.facebook.com/groups/1232550283531628















BANI NA KASHE TABA 😫🔫.



  Na big boy isah


.  *DEDICATED TO YOU 5STAR ✨✨ ASSOCIATION*

.


5 star's ✨✨ online writer's association 👌


.
Part 45












suna isa asbiti aka yi saurin karban dad akayi emergency da shi domin bashi taimakon gagawa. abba da deeny kasa zaune sukayi tsayuwar ma gagara tayi sai zirga zirga da suka hau yi.  a can kuma cikin gidan alhj tsit kake ji ba wani mai kuzari a cikin su domin alhj sanusi ya kira ya shaida musu halin da ake ciki shi yasa dui suka damu wasu na kuka wasu na jimami hajia saratu kam kuka take yi sosai bata taba tunanin wai danta zai iya kashe ko kaza ba balle mutum uwa uba ma wai yau dadyn sa zai bayar. cike take da takaici iri iri. su haleema kuwa dake sun san komai dama basu wani wani ji mamaki ba aneey kuwa lokacin ta tabbatar da lbr da suka bata gaskiya ne  haka dai gidan ya kasance har yamma shiru kake ji ba wani mai walwala a cikin gidan. su dady kuwa suna asbiti jikin alhj yayi sauki sosai domin sun hadu da kwararun likitoci tuni suka magance matsalan. shidai kawai tsitar kansa yayi a gadan asbinti a kwance gashi baiji wani gu a jikin sa na mai ko alaman ciwo bama.hkn yasa da abban haleema suka shigo ya fara aika musu da tambayoyin cewa wai me ke faruwa da shi me ya kawo shi hospital ina yazeed nan suka shiga kwantar mai da hankali a kan ya natsu bayada lfy yana bukatar hutu.. amna shi ina shifa lfy sa lau yake gaya musu. lokacin ne wani doctor ya shigo hannun sa dauke da wasu takardu nan yake sanar musu cewa an sallame sa zasu iya tafiya dama ba wani abu ke damunsa ba kawai alluran da aka mar ne abun ya wuce ka'ida. nan dai sukayi du abunda ya dace. suka taho gida duk abunda akeyi dpo na tare da su...



bangaran su yazeed kuwa ranar sunsha azaba iri iri wacce ma basu taba tunanin kalarta ba domin sojojin nan kalan abunda suke musu sun gwammaci mutuwa ma a kan haka. lokaci daya duk aka canza musu kamanni. gaba daya baraka iya gane yazeed ba. haka suka sako shi a mota suka nufo gida da shi.

su abba kuwa a babban parllon gida suka hadu kam jama'a gidan nan dpo ya mike yaki. musu jawabi a kan duk abunda yake faruwa tun daga lokacin da suka kama deeny har zuwa ynz. sannan deeny ya mike shima yayi salama. farinciki cike a ransa. nan ya fara basu labarin duk abunda ya faru duk yan wajen saida suka tausayawa deeny mahaifiyar sa kuwa sai kuka take tana dada tausayawa yaran nata. hk itama haleema abun ya kasace. nan deeny yake fada musu duk abunda yaji a bakin yazeed na cewa shine ya sa a kashe su haleema da kuma kyautaf dadyn sa da yayi ga dodo. alhj yayi mamaki sosai da jin wannan zance wato ynz dama yazeed duk tarbiyar da muka mai a banza kenan ta tashi ynz dama kudin da suke shigo mai yna fakewa da kasuwanci ashe dama ta wannan hanyar yake samun su. hk dai yaci gaba da tunane tunane. nan shima isah ya mike ya bayyana komai dangane da tsintar halima da yayi hk kuma abun da deeny ya fada shima daidai ya fade shi bai ko saba ba. nan dai kowa yaci gaba da bada lbrn sa duk aka cika da mamaki sai dai har ynz an rasa wane laifi ne su haleeman suka wa yazeed har da ya kudarci daukan fansa da ransu. haleema kam tsoro taji ya kara shigan ta ta kasa fadar gaskiya lokacin da aka tambaye ta meye suka mai. maryam ce tayj bayanin komai cewa dakinsa suka shiga alhalin ya kuma suka dauko laptop dinsa to anan ne suka gane cewa ba mutumin kirki bane taci gaba da cewa kafin mu fito ya ritsemu a daki sannan ya mana duka hade da kashedi karmu kuskura mu bayyana idan ba haka ba kuma duk zai hallaka mu shi yasa duk muka tsorata muka ki fada.



kowa ya cika da mamaki a gun. ba'a fi 3mint  ba sai ga yaxeed sojoji sun shigo da shi kallo daya xaka mar ka gane cewa ya lakadu .




durkusar dashi sukayi a gaban jama'a a cewar su wai suyi bankwana da shi. maman sa kuka ta shiga yi ganin halin da dan nata ke ciki sabanin dadyn sa da yake jin wata tsanarsa kmr yaje yasa bindiga ya harbe shi a gun jama'ar wajen kowa yayi allah wadai da halin yazeed shima yazeed sai a lokacin yake nadama shiga wannan kungiyar bayan bai rasa ci ba bai rasa sha ba kudi suna shigo mai ba laifi amma san zuciya da san tara makudan kudi yanzu sun kaishi ga halaka. a lokacin duk wanda ya kalli yazeed zai gane yana cikin ladama. ko bakayi niyar tausaya mai ba sai ka tausaya mai cikin kuka da wata murya ciki ciki yake cewa ku yafe min dan allah ku yafe min nasan na jefa rayuwar ku ku duka cikin wani hali amma sai yanzu nake cike da ladama wanda nasan ko  kun yafe min ba lalai ne in sama rahamar allah ba amma yafiyar kawai nake nema a gare ku. wajen tsit yayi kowa ya tausaya mawa yazeed domin yayi nadama.



halima ce ta fara daga baki tace ni dai na yafe maka duk abunda kamin ya yazeed allah ya yafe mn ga baki daya sanda hawaye suka kwaranyo mata. kowa yayi mamaki a gun shi kansa baiyi tunanin halima ce zata fara yafe masa ba. daga jin haka maryam itama ta daga baki tace ta yafe duniya da lahira. wannan ya faranta ran yazeed sosai. hk yasa kowa ya ta yafe masa. duk kowa ya yafe har ummansa itama dsdyn sa ne kawsi yayi shiru bai ce uffan ba.


abba idan baka yafe min  ba bansan halin da zan kasance ba. bana so in tafi ba tare da yafiyar ka ba dady ni nasani cewa tawa ta kare domin kuwa koda ace basu kashe ni ba ni nasan cewa yau bazan kwana ba domin ka'idar kungiyar mu kenan mun karya alkawarin dan hk bazai kyale ni ba duk wani dan kungiya dole ne yau ya bakunci lahira.......................

TAMBAYA IDAN KAINE DADY ZAKA YAFE KO KUWA?????? nidai nace.....

morng to u oll my frnds 🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽  👑king boy 👑na gaisuwa


Bi wannan line din domin join na grp dinmu  ko ka/yi  search insa BIGBOY ISA NOVELS

https://m.facebook.com/groups/1232550283531628
















BANI NA KASHE TABA 😫🔫.



  Na big boy isah


.  *DEDICATED TO YOU 5STAR ✨✨ ASSOCIATION*

.


5 star's ✨✨ online writer's association 👌


.
Part 46









hakika yabawa dady matukar tausayi baisan lokacin da idanonsa suka ciko taff da kwalla ba nan ya dinga tuna abubuwan da yazeed yake musu na alkhairi wannan kawai sharrin shaidan ne. na yafe maka yazeed allah ya yafe maka. hk ya furta yayin da tuni hawaye sun gangaro fuskansa sanda yake kallan yaran nasa. cike da tausayi. cikin wata irin murya mai karkarwa yake cewa na gode dady sannan ya fashe da kuka a wajen ba wanda bai tausayawa yazeed ba. nan wani soja yace kana da mgn ko kuwa ka gama. na gama yallaba ynz abunda zance shine ya kalli dadynsa. sannan yace a kwashe kaf kayan dakin can sanda ya nuna dakin da yatsa wato dakinsa yace gaba daya a toya hk ma dakina na can abuja shima a kwashe kayan kaf a toya. yana gama fadin hk chamaf wasu sojoji biyu sukayi sama da shi suka fara tafiya. yana kuka yana tsulle2 ake tafiya da shi. hk itama mahaifiyar sa kuka take sosai tana wa dan nata kallan karshe. ( rayuwa ka aikata mai kyau duk wuyan sa duk dadi idan kayi sharri kai zaka girba abunka a lokacin zaka ji dadi sosai saida lokaci yana zuwa wanda zakayi kuka. allah yasa mu dace ameen. )





gaba ki daya dai gidan hk ya wuni ranar nan ko abincin kirki ba wani wanda ya sama damar ci saidai tattabawa.

aliyu kam zaune yake shi kadai ya rasa meke mai dadi shifa a gaskiya san anney yake gashi ya kasa gaya mata karfa yayi zurfin ciki. nan ya dafe kai yana tunanin shi ya zaiyi ya bayyanawa wannan yarinyar yana santa domin kuwa idan ta koma kauyan su baya tunanin zai sake ganin ta gashi yana ji yayan ta ya takura shi gida yake so ya koma. tashi yayi da sauri ya nemo paper da bairo ya rubuta wasika. yar aikin gidan yabawa ta kai mata sannan ya kwatan ta mata anney yace ta bata a sirince kar ta bari wani ya gani. ta karba.



deeny ma fa haka al'amarin shi duk wannan al'amarin baya damunsa tun dazu bayan sun hadu da maryam da mamansa yaji wani fayau ba abunda ke damunsa ynz masoyiyar sa kawai yake san gani saidai ya rasa ta hanyar da zai kirawo ta domin su hadu da juna bayan uban missing inta da yake ciki. itama hk taji ba abunda take so ynz sai ganin deenyta cikin parlloo  suke zazaune sun kunna tv amma ba wanda hnklinsa ke kan tv kowa ta tasa yake yi. halima sai yan kifce kifce take hakan yasa ummanta ta gano ta. tace uhm wato gurinsa kike so kije shine kika kasa fada ko to ai ni na ganoki tashi kije wa zai hanaki ganin deeny kuwa. fuska ta rufe ciki da kunya tana murmushi ta yo waje bisa mama ki a kan wani dan dakali ta tarar da deeny inda dama sun saba haduwa a gun nan fa aka sha hira irin ta masoya. an dade ba'a hadu kuwa yana nuna kalan damuwanda ya shiga dalilin rabuwa.

karfe 10 sukayi bankwana kowa yayi bangaransa.


 isah kam yaso ya koma gida yau amma ganin halin da gidan yake yasa ya hakura amma yasan cewa iyayansa barasu ji dadi ba kawai dai yasan idan ya fada musu abunda ya faru zasu mai uziri. kwance yake yana wannan tunanin a cikin dakin da suke shi da aliyu da kuma deeny. sai ynz yama tuna da ya hardace number salmanu cikin hanzari ya tashi aliyu yace ya aro mai waye. shima aliyun bai yi barci ba tukun yana nan sai tunanin sahibar sa yake. nan ya miko mar wayan. yayi dial din number salmanu amma is switch off.hk ya hakura yabawa aliyu wayarsa shima ya kwanta.


anney kuwa  har ta kwanta kuma sai ta tuna da wasikan da aka kawo mata cikin hanzari ta tashi ta dakko ta tazo ta tashi su halima wai su karanta mata. kai anney wllh bakya jin mgn ynz bazaki barmu muyi barci ba mu hutawa ranmu. inji maryam .sannu matar yaya kwanta kiyi barci ni nama isa in hn aunty na barci. pillow din dake wajen ta ta dauka ta wurga wa anney hade da cewa wannan kanwar tawa bata jin mgn. suka yi dariya gaba daya.  anney ta mika mawa haleema pepar karanta min wannan. haleema ta karfa takardan miye wannan lokacin da take warwarewa. kedai kawai ki karanta. hmm tace sannan ta fara karantawa kamar haka. ((    assalamu alaiki bayan gaisuwa mai tarin yawa tare da kin wani cikin koshin lafiya gimbiya aneesat farar mace alkyabar mata yar mutunci da kima. halima ce ta dan tsaya da karatun ta kalli anney tana mata murmushi. ita ma martani ta mayar mata. maryam ma haka ta matsokurkusa dan jin waye ya aiko wannan later. sannan halima taci gaba da karanta musu. a hakikanin gaskiya na fada katan kogin kaunarki tun kallan farko da namiki nake tunanin ni dake mun dace tarbiyarki da natsuwarki da sanin ya kamatar ki sun mini aneesat. saidai bansan ko zan sama masauki wato gurbi a zuciyarki ba. ki bani dama in nuna miki so da kauna da kulawa ina san ki zama mallaki na uwar yayana ki zamo mai share min hawaye na karki sa su zubo aneest. nasan zakiyi mamakin ji nine na aiko da wannan wasika amna ta wani bangaran ba abun mamaki bane domin shi so baya buya kuma so makawo ne. daga karshe dai ina kuma jadada miki so da kaunar da nake miki i love u aneesat.  from aliyu to u.... i waiting reply 4r u bye2... nan fa anney kunya duk ta cika ta kai ta totsa cikin blanket. tana dariya. zolaya dai ba irin wace basu mata ba daga baya suka natsu. maryam tace to ynz fda mana. kina san sa ko aa. haleema ce tasa hannu ta dan bigi maryam tare da cewa ke ina ruwanki. maryam tabe baki tayi sannan tace to miye laifi na ai gwara a fada mn domin musan matsayin mu. hka dai sukata surutan su ita kam aneey bata sa baki ba bata ce musu ko uffan ba. nan suka gaji har suka kwanta bata basu amsar eh ko aa ba.



washe gari tunda sasafe bayan anyi breakfast wajen karfe 8:00 kowa ya taru a katan parllo kawu ake jira kawai ya karaso................

ayi min afuwa ban sama damar post ba jiya..

afternoon to u oll my frnds 🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽  👑king boy 👑na gaisuwa


Bi wannan line din domin join na grp dinmu  ko ka/yi  search insa BIGBOY ISA NOVELS

https://m.facebook.com/groups/1232550283531628












BANI NA KASHE TABA 😫🔫.



  Na big boy isah


.  *DEDICATED TO YOU 5STAR ✨✨ ASSOCIATION*

.


5 star's ✨✨ online writer's association 👌


.
Part 47








bayan kamar minti sha biyar sai ga kawu ya iso baya sun gaisa da abba da kuma alhj bashir. sai kuma su maman deeny da su maman haleema suka gaishe shi. sannan suma su deeny da su anneey suka gaishe su. toh bayan anyi gaishe gaishe ne kuma  guri yayi tsit ana jira aji abunda abba da alhj zasu fada domin sune suka kira taran. abba ne yayi sallama kowa ya amsa sannan ya zarce da bayani. to da farko dai ina so ku sani cewa duk abunda ya sama mutum na dadi ko kuwa sabanin hk to kaddara ne da kuma jarabta daga allah allah shi yasa ake san musulmi a ko'ina ya kasance mai hkri da juri. sannan ina bawa yayana alhj bashi gashi tare da matarsa hakuri bisa rashin dan su da sukayi wato yazeed domin kuwa yazeed a halin yanzu ba abunda yake bukata daga gare mu sai addu'a duk da cewa yazeed ni sanadiyar shigar mu wannan hali hkn bazaisa muki masa addu'a da kuma fatan samun rahama a wajen ubangiji. jawabin abba yasa kowa natsuwa a wajen kuwa yayi tsit. ya kalli isah yaci gaba da cewa hakika batan yarmu yasaka mu damuwa sosai bama kamar mahaifiyarta da ta dinga nema ta fita  a hayyacin ta. hkn tasa nayi alkawarin gagarumar kyauta ga duk wanda ya kawo min di'yata. haka zalika har yanzu alkawarin nanan bai tashi ba. dan haka karbi wannan ya miko mar key da kuma wasu takardu. hade da cewa wannan kyauta ce daga gare ni wannan takardu na daya daga cikin manyan gidajenane dake nan baya. wannan kuma makullin mota ne shima na baka sannan ina so ka zaba kalan sana'ar da kake so ni zan baka jari. bayan nan ka zaba matar da kake so a nan ko a can garin ku ni zan shige maka gaba. ko yar gidan waye. dago kai yayi daga sunkuyan da yake ya kalli maryam yayi da suka hada ido murmushi ya sakar mata. itama murmushin take. to abba na gode2 allah ya saka allah kuma ya kara karewa. nan dai yata mar godiya kala2 tare da addu'o'i. abba yace ba ya isa hk ai kai xamu wa godiya tare da duk ahalinka domin haleema ta bamu lbr irin rikon da iyayan ka suka musu ita da maryam. ko ta nan mun tabbatar da mutanan kirki ne da zasu yarda ma da sun dawo nan abunsu munci gaba da zama. isah murmushi kawai yayi ranshi cike fall da farinciki ynz burinsa ya kusa ciki zai auri maryam dama abunda zai hanasa auranta shine idan ba'a nan garin zai zauna ba.. nan dai yata tunani yana murmushi hade da mika godiyarsa ga allah...



bayan an danyi shiru ne kuma alhj bashir shima ya mike kamar hk shima kyautar katan gida yayi wa deeny bisa cetan rayuwarsa da yayi. sannan ya taimabaya su aliyu suna da wa'ina suke so ne? kunya ce ta ishesu. sai deeny da yake murmushi ganin sun kama yan nuke nuke. a zuciyarsa yace wllh ynz zan tona asirin kowa.  matsawa baya yadanyi. yana dariya yace abba ai dukan su yan matan nasu suna cikin gidan nan. a cikin rashin fahimta alhj yace ban fahimta ba fahimtar dani. nan deeny ya dan natsu yace shi dai wannan kanina ne wato shi maryam yake so shi kuma wannan brox din wato aliyu zurfin ciki ya hana ya bayana cewa yana san aneesat. ai kuwa dariya kowa ya fara yi aliyu da isah kunya ce ta cika su hk suma su maryam.kunya..aliyu kuwa sai hararen deeny yake.  bayan an dan saurara ne alhj ya juya kallansa zuwa ga anney yace yata kinji dai abunda ake ciki to ynz ki fada mn gaskiya karki boye mana muma a matsayin iyayanki muke shin kina san aliyu ne ko kuwa akwai wani a wanda ya riga sa a fada mai ya hakura. aliyu kuwa gabansa ne ya fadi cike da fargabar amsar da anney zata bayar. babu kowa. kawai ta fadi hade da rufe kanta da mayafi ta tashi ta ruga dakin haleema cike da kunya. dariya tabawa mutanan gun. shi kuwa aliyu wani farin ciki ne ya lulube shi nan ya kama hamdala yana godewa allah.
alhj ne yace to alhamdulilah yanzu dai abunda ya kamata shine ya kalli isah kai kaje ka shaidawa iyayanka duk abunda ya faru. domin kaji ta bakin su idan suna so su dawo nan to idan kuma acan suke san zama to duk dai zabi ya rege gare su. mudai muna neman diyar su wato aneesah sannan muna rokon allah ya kara hada kawunan mu ya kuma sa mu dace. ameen kowa ya amsa. alhj yaci gaba da cewa ni gudun muwata a wannan biki ga amare ne ni na dauke wa iyayan su nauyin  kayan  daki gaba ki dayan ku ku uku. alhj sanusi ne yace ah abun haka ne ko to ni kuma na dauke wa duka angunan sadaki da kuma gidajan da zusu zauna duk kan su ukun. nan suka hau godiya da sa albarka kawu ma yayi farinciki sosai domin dauke mai nauyi da akayi har uku wato deeny da maryam wanda shine kanin mahaifin su ga kuma aliyu. nan yayi godiya sosai ga alhj sanusi da kuma alhj bashir nan aka dan taba hira sannan isa ya tashi ya shirya domin yaje ya sanar da iyayansa. anney kuwa umma ta hana aje da ita wai a barta nan za'ayi gyaran amare ba. inda zata hk dai isan ya hakura ya tafi shi kadai domin sanarwa iyayen nasu kuma yaji hukuncin da zasu yanke.............

.. bigboy isah ♥














BANI NA KASHE TABA 😫🔫.



  Na big boy isah


.  *DEDICATED TO YOU 5STAR ✨✨ ASSOCIATION*

.


5 star's ✨✨ online writer's association 👌


.
Part 48 to END







batun yazeed kuwa da aka tafi dashi dake dare yayi cikin wani daki aka saka shi wanda ake saka masu laifi. da safe da suka zo suka duba tarar da shi sukayi ya mutu bakin sa na zubar da wani kalan abu baki kirin kamar an daka tawada haka kuma ya wani kun bura kamar zai fashe. basu shugaban sojojin dpo ya kira ya sanarwa da hakan cikin gagawa ya nufi gidan alhj sanusi. ganin yanda gidan ya cika da farin ciki da murna yasa bai fada musu halin da ake ciki ba suna gaisawa ya juya zai koma nan alhj ya kira sa ya mai kyaututuka. nan ya fahimci su tuni sun ma manta da  dan nasu shi yasa ma bai fada musu abunda ke faruwa ba dan karya tayar musu da hankali.


washe gari bayan isah yaje ya bayana wa iyayansa duk abunda ya faru sannan ya bayana musu mgnr auren sa da kyaututuka da abba ya mishi da kuma auren shi da ma batun anney sannan kuma ya nemi su da su koma birni tunda ba abunda suke yi a kauyen har kaka zasu tafi.
iyayan isah kuwa sun amince da zasu dawo birnin ummansa ne ma da taki yarda daga baya kuma da suka bata baki saita amince. duka sun tarka to yan kayan su. a gidan da abba ya basu nan suka sauka. gida ne isashe ba laifi ya isa suyi iya rayuwarsu nan suma suka gode wa abba. bayan sunyi wanka sun huta ne isah ya dauke su a mota da yake dama ya iya da ita yaje dauko su ma a kauye yan kauyan sun taya shi murna sosai suma.


nan ya kaisu gidan alhj ya gabatar da su anney tayi murna sosai ganin mahaifiyar tata da kuma kaka. nan isah yake bayyana wa abba  cewa iyayansa sun amince sun dawo nan domin ynz na kwaso kayan su ma mun dawo nan. kowa yayi farin ciki sosai da jin haka. nan aka tashi yaran wajen ya koma sai iyayen. nan akaci gaba da tataunawa mgnr aure. nawa za'asa shi. kawu yace hh tunda dai yara nasan junan su kuma iyaye duk mun amince dan haka ba sai an dauki wani tsawan lokaci ba kawai asa auran nan sati daya kafin nan kowa yayi abunda ya dace. kowa ya amince da mgnr kawu nan aka shiga shirye2 aure amare kuwa sai gyara ake musu. kafin sati ya cika a kwana a tashi ba wuya wajen allah yaune sati ya cika kuma yau ta kama asabar daurin aure. anyi taro sosai anyi sha gul gul. wanda lokaci bazai bani damar bayana muku irin abubuwan da akayi a cikin wannan sati ba saidai in yanke muku gun kawai sbd tsaro...
anyi komai anyi taro iya taro an daura aure amare uku su duka ukun kaya kala daya suka saka. ba abunda zai burgeka sai ma kaga gida jen da abba ya basu a jere suke daidai  wadaida du su ukun. fenti da komai da tsare2 gidan du kala daya ne. kutt haka ko wace kawayen ta suka rakata gidan ta. kai al'quran  na gaji hhhhhhh lol. gida dai ya kara girma ya cika da farinciki zaman lfy ya suke su duka ukun suna shan soyaya abunsu. ":;/




ALHAMDULILLAH!!!!!

A nan wannan labarin yazo karshe ina fatar masu karatu kun samu darussa, nishad'i a ciki.Wannan littafi na BANI NA KASHE TABA.
  Sadaukarwa ne gareki
NADIS my only one allah ya bar kauna.

KU KASAN CE DANI A SABAN LITTAFINA MAI SUNA ♥ SAN GASKIYA♥
.


KASAN CEWAR WANNAN SHINE LITTAFI NA NA FARKO NASAN DOLE NE NAYI KURA KURE DA YAWA A CIKI DAN HAKA SAI DAI IN BAWA READERS HAKURI A KAN HAKAN SANNAN INA SO SHAWARA A GARE KU ABOKAINA. DOMIN RUBUTUN YANZU AKA FARA
  DOMIN BANI SHAWARA
WHATSAPP NUMBER = 08096831009
OR
INBOX ME
OR CALL ME 08096831009


bazan manta daku ba masoyana masu kuma san ci gabana.
yan groups din face book da na whatsapp=
JINJINA A GARE KU:

PHARIDA KAMSHI NOVELS

SAME KHAIRI NOVELS

HOME OF NOVELS

HOME OF HAUSA NOVELS

FILIN LITATTAFAN HAUSA

HAUSA NOVELS

3STAR HAUSA NOVELS BY KING BO

HAUSA NOVELS BY KING BOY

HUSNAT NOVELS


360novels

kai dama duk sauran groups wanda na fada da wanda ban fada ba.. king boy na gaisuwa

BAZAN MANTA DA KU BA

ZEESA NASMAT AMA ALHJ KABIR AND NADEEYA .

MARYAM

MARYAM SHEHU ADAM

RUKAYYA ALHJI

Aminu Tajuddeen Suleiman


Fatima Adamu

Muhammad Nura

Mardiyyatijjani Mardiyyatijjani

Amnat Bashir Lere

Maimuna Madara

Nanah Muh'd

Rahmatu Gimbiya Umar


fauziyah salami


dama duk wanda ban anbata ba
naku har kullum kingboy ko kuce bigboy isah sai mun hadu a post na gaba
LUV YOU OLL 
adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *